TYPING 📲 FRI, 18/23 08:️20AM YUSRAH MUSA ABUBUKAR ✍️. 👑 ROYALTY 👑 WHATSAPP NO:234 8160983083. I'm back Na dawo is my time whow missing me ku fito mu kwashi nishad'i yadda ya kamata. IN THE NAME OF ALLAH THE MOST BENEFITS AND THE MOST MERCIFUL ALLAH SWT THE MOST HIGH IS PURE HE ACCEPTS ONLY WHAT IS PURE ALLAH THE MOST HIGH DOES NOT SLEEP WE LOV OUR NABEE WE LIKE HIM NO SUCCESS WITHOUT HIM HE'S THE MIRROR OF OUR LIFE HE HAVE NO LIMIT, PEACE BE UPON HIM AMEEN. DEDUCTED TO My Late father😭 }{MUSA ABUBAKAR IBRAHEEM}{ ubangiji Allah ya gafarta maka Allah yakai haske cikin 'kabarinka Allah yayi maka rahma. Ibrahim Musa Abubakar Aishat (Ummi) Musa Abubakar Abdullah (Adali) Musa Abubakar. 😭Ubangiji Allah ya ji'kanku da rahma Allah yakai haske 'kaburburan ku ina ro'kon Allah yasa aljannah ce makomar ku Amin. Yusrah Musa Abubakar Saleem Musa Abubakar Naja'at Musa Abubakar Aishat Musa Abubakar Fatima Musa Abubakar Abubakar Musa Abubakar 😥Mu kuma ubangiji Allah ya bamu ha'kurin rashin mahaifin mu da 'yan uwan mu Allah yasa idan tamu tazo mu cika da imani alfarmar sayyidina muhammadur rasulullah SAW Amin. ÀÑÑÙRÌ WRITER'S ÃSSÕÇÌÅTÍÔÑ 💫 HOME OF HOSPITALITY AND HARMONY gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai 'ya'yan ta. STORY WRITTEN ND EDITING Yusrah Musa Abubakar Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë. 🕋🕌🕋 It's Friday don't forget to recite suratul al-khaf may Allah open the door of success 4 all of u Muslims in the world amiinn. Yusrah Musa Abubakar (YUSEEN AL-AMEEN CE 📝📚✍️WRITER👇 YARIMA ABDUL-MALEEK RAYUWA BIYU SAFREEYYAH 'DAN MILIONAIRE MINAH-UMER DAMA KECE ZUCIYAR ALIYU CE HUSNAH KO BADIYAT YARIMA ARYAN ME KAMAR SARKI TAJUDDEEN ARYAM MINISTER ASHRAF ANDNOW...........📚✍️ 👑ROYALTY👑 I wish to thank Allah swt for the opportunity he gave me in putting across another book,🙏 royalty is a book that entertains educates and informs,, alhamdulillah ala kullu halin may the blessings and the peace of Allah swt be upon to our prophet NABI SAW no success without him he's the mirror of our life he's the answer to every question he've no limits ya rasulullah. 1️⃣Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil mursalina. @YUSRAHMS CE NO: 01 to 02 Tsaye wani zu'keken saurayi yake fari tarr dashi a cikin wani dan'kareran tsararren parlor wanda ya wadatu da kayayyaki na alfarma irin na sarauta da wata had'add'iyar budurwa kyakkyawa dur'kushe a gabansa tana kallonsa cikin tashin hankali ta toshe bakinta da hannu dan kada kukan da take ya fito fili sai hawaye dake ta faman ambaliya a fuskarta ransa a mugun 'bace cikin tsawa mai firgitarwa ga mai sauraron sa yace. "I said stop look me like that what are you doing here"?. Jikinta ne yadau rawar tsoro da tashin hankali ga zafin da bayan ta ke mata dalilin dukan dayai mata da belt. "What am I supposed to do? me zanyi Baby ba dake nake magana ba zaki fad'a min ko sai jikin ki yayi tsami, uban wa yasa ki d'aga min waya har ki samu damar magana na saki ne"?. Kai kawai take iya girgizawa ta kasa magana tsabar tsananin tsoro da irin bacin ran da take hangowa a cikin kyawawan idanuwansa. "Baki da baki"? ya fada yana sake sauke mata wannan gardiyar belt d'in irin wacce sojoji ke d'amara da ita a bayanta da karfi dan a duniya ba abinda ya tsana yake saurin sa ya fusata kamar ya maka magana ka bashi amsa daka ranar kuwa da saika wuni ka kwana kan yana ciwo saboda azabar dazai d'andana masa wacce bazaka sake marmarin masa laifi ba shiyasa yanzu hankalinta ya tashi zuciyarta tahau bugawa da 'karfi. "Nace baki da baki kin kurmance ne baki gane yaren da nai miki magana dashi baa"? Ya karasa maganar a fusace yana sake zuba mata belt d'in a gadon bayanta. Zatai ihu ya daka mata tsawa wacce yasa ta sake susucewa a hargitse ta mi'ke zata gudu ya dam'ko ta tare da murde mata hannu da 'karfin da yasan zataji ciwo ihu ta kurma da karfi itama tana faduwa qasa cikin azaba ta fashe da kuka ta rasa inda zata sa kanta taji sassauci ko'ina rad'ad'i yake a jikinta tsuka ya ja zuciyarsa na qara ingiza shi tana tado masa da sabon fushi a kanta kallo d'aya ya mata yana tsallake ta yabar parlon ya koma bedroom yana cewa cikin kamammiyar murya mai dad'in sauraro. "Idan jikin ki ya fad'a miki yau gobe ko ance ki d'aga min waya baza ki d'aga ba yarinya karama sai rashin ji" haka ya shige part dinsa ya barta kwance tana juyi a kasan carpet. Kai prince Hamid dake zaune ya girgiza yana mi'kewa yaje inda take ya d'agota dan bashi da ikon hana Ahmad ya hukunta ta kuma da yasan abun zaiyi zafi har haka daya hanata d'aga wayar ba tare da yace mata 'kala ba kawai data mi'ke tsaye ya saketa yabar parlon yabi bayan Ahmad yaje ya masa magana a kanta yana shigewa ta share hawaye da'kyar ta d'aga qafarta ta fara takawa a hankali cikin d'ingishi ta fita tana shiga part dinsu kallo d'aya Mami dake kishingid'e tai mata tana d'auke kai batace komai ba ta mayar da hankalin ta kan TV kamar bataga a yadda ta shigo ba saidai tasan duk fad'in gidan babu wanda zai mata haka bayan Ahmad shiyasa ma bata tanka ba itama babyn batai magana ta wuce tana shiga bedroom ganin babu kowa kila Aunty Khairat ta fita yasa tana zuwa ta fad'a kan gado ta kwanta tana cigaba da kukanta tunda tasan babu mai ce mata tayi shiru balle a lallasheta dama Abbansu yana nan ne ko Abban su Ahmad d'in su kad'ai ne zasu lallasheta zuwa 'bangaren Sultan Sharfaddeen (Mai Martaba Sultan Ameer) kakansu a yanzu zai bata wuya kan taje domin tafiyar da nisa kamar ba gida d'aya ba yake da nisa dasu kafin kaje fadarsa haka suke da rata sakamakon gidan sarautar nada girma na gaske ga kyau da tsari abun burgewa. Sau'ke ajiyar zuciya mai zafi tai tana mi'kewa taje jikin mirror ta fara kallon kanta a tabkeken mudubin ganin yadda yai jaa duk inda ya daketa ya shata kamar jini zai fito yai tsartuwa domin fara ce tar-tar kuma kaf yaran gidan babu wanda ya d'auko fuska irinta Ahmad yake kama dashi sai ita ko Khairat da suke uwa d'aya uba d'aya dashi basa kama dashi kamar yadda ita suke kama amma ya rasa wanda zai ri'ka zalunta yana hukuntawa sai ita¿ d'an tsaki taja kamar kuma an tsikare ta a firgice ta juya tana kallon qofa tsoro 'karara bayyana a kyakkyawar fuskarta gani take kamar inta juyo zata hada ido da Ahmad ko zai fahimci wannan tsakin dashi take ganin dai ita kad'ai ce har lokacin babu kowa yasa ta sau'ke ajiyar zuciya tana tunanin wannan wacce irin masifa ce mutum baya guri ma amma tsoron sa yasa takejin kamar yana gun juyawa tai tana shiga toilet ta hada ruwa mai zafi tana gasa jikinta sai yamutsa fuska take tsabar azabar da takeji amma haka ta daure ta d'umame jikinta dakyau kamar wata mai jego ko'ina kuwa jikinta sake d'aukar rad'ad'i yai har saida taji dama batai hakan ba neman maganin zugi take a cikin drawer dake jikin bed din domin ranar taga Aunty Khairat ta shigo dashi tasha itama daya bugeta akan 'karamin abu dabai taka kara ya karya ba iya dubenta bata ganshi ba ta ha'kura gashi jikin nata ya dameta tayi tunanin sa kaya taje gurin prince Hamid ta kar'bo amma saboda tasan zata iya had'uwa da prince Ahmad yasa ta ha'kura kawai ta kwanta cikin dauriya tana cije pink lips d'inta bata sake marmarin fitowa ba balle tabi takan wani abinci har saida akai sallar magriba da isha sannan ta fita parlor inda Mami take bayan ta gaishe da ita ta kwanta ajan daya daga cikin d'uma-d'uman chusion d'in dake zagaye da falon kawai ta lumshe idanuwanta kamar maijin barci ta. Kallonta Mami tai na 'yan sakonni tana girgiza kai kafin ta mayar da hankalin ta kan TV tana cewa. "Baby tashi daga kwanciyar nan ki kaiwa yayan ku abinci yanzu naga takwas tayi kar dare yaja baici ba kinsan indai goma tayi ya ha'kura komai son da yakewa abincin zai barshi tashi maza kije a had'a miki ki kai masa". Tashi zaune tai bayan ta gama jin me Mamin tace idonta ya cika da hawaye jikinta ya dau rawar tsoro lokaci guda ta fara kuka harda yarfa hannu taya zataje gunsa a yau aiko gobe bata fatan su had'u dashi balle tun a yau da komai bai lafa ba. Wani kallo Mami tai mata tana cewa "meye haka? wannan shashancin kuma fa kukan na mene"?. Cikin muryar kuka take girgiza kai tana kallon kofar shigowa gani take kamar shine zai shigo ko yana jinta tace "Allah Mami tsoro nake ji bazan iya zuwa gurinsa ba yad'au fushi dani sosai dan Allah ki taimaka min ki aika Sultan". 'Dangowa Mami tai tana qare mata kallo da karantar yanayi na rud'u da rawar da jikinta keyi tace "na aika Sultan Saboda da me? Bayan gaki"?. Goge hawayen fuskarta tai tana cewa "Mami idan naje zai karya min 'kafa wallahi nasan ba ha'kura yai ba". "Oh ya karya miki qafa? A'a kin manta ba 'kafa zai karya miki ba kashe ki zaiyi,, kinsan Allah baby ki kiyaye ni zaki tashi ki kai masa kibar wannan shirmen 'bata lokacin ko saina bige ki a haka ma ba tsira kakai ba maybe kiyi latti wajen kai masa kinga kin 'bata biyu baki wanke biyar ba kin 'bata goma kinsan kina jin tsoron nasa kikai masa laifi"?. Tana shashshe'ka tace "Mami ba laifi nai masa ba kawai dan an............... Katseta Mami tai da cewa "na tambaye ki mene abinda ya faru tsakanin kune? Ta tashi ki kaima abinci baby kafin ki jawa kanki wata wahalar kinsan ko a rami kika 'boya saiya 'kwa'kulo ki da ace yaga damar qara miki wani dukan ina zaune a parlon nan zaizo ya wuce ya nad'eki ba ruwansa to tunda kinsan haka ne dan me zaki zauna kina kwane-kwane just ki tashi kikai masa idan kin manta bari na tuna miki kina qara wasting time dinki wajen kai masa kinga idan kika d'ada kuskure ya jibgeki acan gobe saiki hanyar ma'kabarta ko". Kukan tane ya karu sosai ta d'ora hannu aka dan tasan ita kam tata tazo karshe da'kyar ta mi'ke kamar mara lafiya ta soma takawa ta nufi hanyar fita dan dakatawa tai tana sake juyowa ganin idon Mami a kanta yasa cikin muryar tausayi tace. "Dan Allah Mami kiyi hakuri bazan iya zuwa inda yake b.............. Bata karasa ba a tsawace Mami ta katseta "get of my sight baby kafin na fusata". Fita tai tana kuka had'uwa sukai da Sultan zai shiga part d'insu ganinta haka yasa yace. "Aunty baby wai har yanzu ke da yayan ne mai kikai masa kuma yau"?. Share hawaye tai tana kallon sa bata bashi amsar tambayar saba sai cewa tai. "Sultan ka taimake ni ka kaiwa yaya abinci idan naje saiya kusan kashe ni yau nasan ba hakura yai ba". Zaro ido Sultan yai wanda kana gani alamar tsoro ne 'karara ya bayyana a fuskar sa kallon gefe da gefen part d'insu yin 'kasa da murya yace. "Wallahi bazan iya zuwa gurin yaya yanxu yana cikin fushi ba saboda kwanan baya da Aunty Khairat tai masa laifi yana bedroom Mami ta aikeni nakai masa healthy spinach mix dayace a masa ina shiga wata tsawa daya daka min bansan lokacin da nayo tsalle na fito a d'akin ba sai gani kaina nai a falo da gudu ta baro part da'kyar nai barci a ranar saboda gani nake kamar biyoni zaiyi". Dammm baby ta sake jin gabanta ya fad'i muryar ta na rawa tace "Sultan nasan baka so ya kasheni dan Allah ka kaima masa yau d'in ma aiba kaine kai masa laifin ba nice iyaci yai maka tsawar ka ceci rayuwa ta". Kai Sultan ya girgiza yana cewa "nima abinda kike gudu shi nakeyi wallahi Aunty baby bazan iya zuwa gurinsa ba da zan iya danaje saboda ke amma nima tsoro nake ji dan Allah kiyi ha'kuri babu abinda zai miki" kafin ta sake magana da sauri kamar walkiya Sultan yayi wuf ya shiga part din Mami. 'Dora hannu tai aka zuciyar ta na bugawa da karfin gaske ta nufi hanyar kitchen tana goge hawaye ta tarar masu aikin suna ciki sanar musu tai su had'a mata abincin ya Ahmad zata kai masa nan danan kuwa suka hada mata komai akan tray ta dauko da niyyar kai masa jikinta na rawa tana zuwa main 'katon parlon daya raba tsakanin part d'in Mami da part Momy da kuma part d'in su Ahmad d'in anan cikin sa'a taga Momyn tsaye tare da prince Hamid da alama magana suke yana nuna mata wani abu a paper dake hannunsa. Wata irin 'kakkafar ajiyar zuciya ta sau'ke tana godewa Allah da sauri ta karasa gurin ta tana dur'kusawa a gabanta ta fashe da kuka mai ban tausayi tana addu'ar Allah yasa daga nan Momyn ta hana ta karasawa part d'in. Kallonta Momy tai da dsn mamaki ita batama lura da itaba saida taji sautin kukants da sauri ta d'agota tana cewa "Subahanallahi baby lafiya me akai miki kike kuka? ko keda Mami ne? fad'a min waye ya ta'ba min ke a gidan nan"? Momy tai maganar tana kallon yadda shacin belt ta fita a bayan hannunta nan take ta gane da Ahmad ne ko ba'a fad'a mata. Cikin kukan tsoro baby take kallon kofar part dinsa dake kulle tana fatan Allah yasa baya nan da'kyar ta d'aga hannunta dake rawa tana nuna wa Mommy cikin shashshe'ka tace. "Yaya ne". "Me yai miki? ko dukan ki yai"?. Kai ta girgiza cikin tsoron kada tace eh Momy ta masa fad'a ya sake d'aukar zafi da ita tace "a'a ba duka na yai ba abinci Mami tace nakai masa yaya Hamid qarfe nawa yanxu"?. Kallonta prince Hamid yai cikin tausayawa yasan tsoro take ko lokacin cin abincinsa ya fita a zahirin gaskiya kuwa Ahmad yana bedroom maybe ma yau bazai ciba duba watch d'in dake d'aure a hannunsa yai yaga tara da minti arba'in batare daya d'ago ba yace "da sauran lokaci kije ki kai masa". Shiru tai ta kasa koda motsi tana jiran jin me Momy zata ce kallonta Momy tai tana cewa. "Baby ko akan haka kike kuka"?. Da sauri ta girgiza kai "A'a Mommy kaina ne yake ciwo" ta karasa maganar tana kokarin boye tsoron ta dan kar Momyn tayi tunanin wani abu. "Ok ayya baby Allah ya sauwa'ke kiyi hakuri ki daina kukan kada ciwon ya qaru je ki kai masa idan kin dawo kizo part dina ki amshi magani kinji". Da'kyar tace "to" tare da daukar turen tai gaba tana shiga part d'in ta wuce dinning table ta aje jin shiru yasa cikin sand'a tana ajiyewa zata fita sai kuma ta tuna ba ai masa haka Khairat ta ta'ba kawo wa bata sanar masa ba yaje har part d'insu ya jawota yasa ta cinye dukkan abincin tana kuka kuma ya faffalla mata mari takai kusan sati biyu a kwance bata da lafiya. 'Dauke numfashi tai tuna hakan da tai yasa dole ta tura kofar bedroom dinsa a hankali tana le'kawa can ta hango shi a tsakiyar 'katon gadon shi yana lullu'be da dukkan alamu bacci yake. A hankali ta sauke wani irin sansanyan numfashi taja kofar ta mayar ta rufe juyawar da zatai taga prince Hamid tsaye a bayan ta yana kallonta kame-kame ta fara zatai magana ta kasa cewa komai sai sunkuyar dakai datai tana mammatse yatsun hannunta kuma ta kasa d'aga qafa tabar gurin gashi ta rasa dalilin ta na tsaiwar shiru tai ko zataji yace wani abu amma dai baice mata qala ba har kusan mintuna biyar haka zuwa shida can tsinkayi muryarsa a qasa yana cewa. "Baby me yasa kika 'ki fad'a wa mum abinda ya faru tsakanin ki da Ahmed kina tsoron ta masa fad'a ne"?. Kai ta girgiza "a'a ya Hamid idan na bari mum ta sani nice zansha wahala shiyasa bazan fad'a mata gaskiyar cewa dukana yai ba nasan yanzu zata hauro bansan me naiwa ya Ahmed ba da nayi d'an laifi koya yake babu d'aga qafa saiya hukunta ni"?. "Babu wani Abu da kikai masa kuma ba tsanar ki yaiba da yake hukunta ki idan kinyi laifi baby baza ki fahimce shiba domin har yanzu ke yarinya ce saidai duk abinda kikasan baya so kina nisa dashi kinga shi ba mutum ne mai son wargi ba". Kai ta d'aga tana cewa "to yaya Hamid nagode zan kiyaye". "Ok yayi jeki". Fita tai tana satar kallon qofar bedroom dinsa tare da addu'ar Allah yasa baiji me tace akansa ba tana tafe tana kalle-kalle kamar wacce take jin tsoro har ta shiga part din momy a palor ta samu Khairat tana karatu zama tai tana huci kamar wacce tai gudu wanda Khairat najin yadda take haki aje littafin tai tana kallon ta tace. "Baby ya dai daga ina kike haka wannan hucin fa kod'ai yauma taku ta had'o kune dan Naga alama keda ya Ahmad yanzu kun zama tom nd jerry"?. Sau'ke numfashi baby tai tana kallon ta tace "humm Aunty Khairat kedai kawai bari aiyau saida na shiga uku a hannunsa banyi tunanin zai barni darai ba😳 yanzu ma daga part din su nake". "Innalillahi baby part d'insu kuma ke d'in me kika yo acan"? yadda Khairat tai mata tambayar tana zaro ido waje yasa ta sake jin jikinta yayi sanyi tace. "Mami ce tace na kai masa abinci". "Oh ina dukka ma'aikatan gidan da bayi masu kula da komai suke"?. "Suna can 'bangaren su kisan dasun gama komai ba zama suke ba komawa yankinsu na bayi suke ni ta aika dan ma nayi sa'a bacci yake iya ya Hamid ne da sauri kuwa na baro part din". Dariya Khairat tai tana cewa "oh ni kam baby kina bani nishadi🤗 in banda abin ki meye zai miki koda idon sa biyu balle yayi bacci duk abinsa ai baki masa komai ba bazai ce zai miki wani abu ba hum'um ya Ahmad me zamani kardai ki shiga harkarsa dan Naga alamarsa da take takensa wannan karon da zafinsa yazo hutu 'karfin samartaka yake ji dashi a banza zai 'ballaki ya barki da jinya. Kai baby ta jinjina alamar rashin gaskiya tana waige-waige tace "hummn aunty Khairat shiga harkarsa ta nawa saidai na kiyaye gaba kefa laifi na masa yau d'in d'azu da yamma". "Laifin me"?. "Kedai bari kawai aunty Khairat idan akace miki tsautsayi baya wuce rana yau shine ya sameni waifa wayar sa ce ya bari a palor kan kujera ya shiga part d'insa ni kuma fitowa ta kenan na zauna banma lura da ya Hamid a parlon ba ana ta kiransa da kiran ya katse wani zai shigo ganin bai fito ba yasa nayi tunanin wanka yake ko bayanan ya fita ne ya manta ta shine na d'aga daga gurin aikinsa ne naji wani na cewa hello Buddy kana jina Ina kasa wayarka inata kira naji bakai pinking da wuri ba"? Jin haka da nai yasa nace "baya kusa mai wayar saidai idan ya dawo" tofa shine yake cemin wacece ke d'in"? Ban lura da ya Ahmad ya fito ba jin abinda ake tambaya ta yasa ya koma part d'insa da sauri nikam na manta wayar boss ce hannuna nake ce masa 'kanwar mai wayar ce................................. Daga fad'in haka naji saukar belt a baya na bansan ya dawo ba ya kar'be wayar ya bugata a bango ta fashe ya rika min tsawa wai uban wa yasa na dauka masa waya har nake magana da wani banzan gardi 'kadagiri ina mace shiba maharramina ba wai dama wayarsa tayi kama da irina 'kananun yara zasu na dauka kiji fa yanzu meye abin qanqanta a jikina shekara ashirin da biyu just ya nuna ban isa ri'ke waya ba man amma sai yace min qaramar yarinya sai shegen taurin kai" ta karasa maganar tana 'kwaikwayon muryarsa. Dariya sosai khairi keyi har da tafa hannu tana cewa "anayi muna jin dad'i ana bari muna jin haushi kai abin nan yayi gaskiya yaya yana burge ni akwai gyara mutum amma kedin da kika san halinsa me yasa zaki dauka masa waya". "To aunty khairat nasan zai dawo a lokacin ne kinsan fa ya Ahmed shi laifi baya masa kadan kalli yadda hannu na yai jaa daya murde min saida na fad'i har kasa ina ihu dan azaba nayi mamaki da ban karye ba". "Humm kinga da kin karye ai da maci kaza nasan haka ya Ahmed zaita sayo wa muna gwangwaje ta". "Ni kuma a barni da wahala ba". Dariya khairat tai tana cewa "To amma baby ya dauke wayar nashi ko har yanzu tana gurin da memory"?. Ta'be baki baby tai "Wallh aunty khairat ban sani ba saidai kije ki duba". Zaro ido khairat tai tana cewa "ni kaza🐔 mijina zakara rufa min asiri na jawowa kaina bala'i abun ya juyo min ya sassanbad'e ni nima balle dama wannan dawowar tashi kafin ya dakeki ni ya fara duka". Sauke numfashi baby tai tana cewa "Aunty khairat nifa bacci nake ji tun d'azu tsoron karna kwanta naji yazo sake hukunta ni yasa na kasa sai yanzu tunda shima yayi barci". "Ok muje sai mu karasa maganar a bedroom" mikewa sukai suna fita zuwa part d'in Mami bata nan ta ciki dan haka suma kawai bedroom duka wuce suna kwanciya dan maganar da sukace zasu qarasa ma bata samu ba bacci kawai suka shiga yi. Washe gari lokacin suna parlor prince Hamid dake kula da Ahmed da yanayin sa ya d'an yi murmushi yana girgiza kai cikin tsokana yace. "Ahmad please ara min wayar ka zanyi amfani da ita yanzu tawa banyi mata chaji ba tun jiya". Da sauri Ahmed ya d'ago ya kalle shi dan yasan bom yake son had'a masa kafin ya kalli Abban su da shima ya d'ago yana kallon shi yace. "Yayanka ba magana yake maka ba ka bashi waya kayi shiru kamar sabon kurma". Rasa abin cewa Ahmed yai sai ido kadai daya zubawa prince Hamid wanda ya kauda kansa yana dariya kasa-kasa. "Hummm bros Hamid is so funny............. Jin Abba yace "Ahmed". "Na'am Abba". "Meke damun ka ne"?. "Babu komai Abba". "Babu komai kayi shiru ana maka magana"? Hamid meke damun sa"?. Gyara zama Hamid yai jin anzo daidai wajen da yake so azo yana kallon Ahmed dake masa magana da ido yai kamar bai ganshi ba. Yace "Abba banace ba amma inaga shida Baby ne". Zaro ido Ahmed yai yana kallon Hamid daya sakar masa hararar gargad'i sannan yaci gaba. "Abba akwai abinda ke damun Ahmed saidai bansan maye ba amma shi Ahmad d'in ya sani ya'ki fad'a". Wani kallo Abba yaiwa Ahmed yana cewa "AHMED what your problem"? Kasa cewa komai Ahmed yai sai bin kowa da kallo da yake har ya dawo kan Abban. Mamaki ne ya kama Abba amma sai yace "shikenan ka samu nutsuwa daga baya zan tambaye ka saika tanadar min cikakkiyar amsa yanzu inada gurin da zanje ina Zuhra da Ummul-khairi suke ko a part Ashraf suka kwana naji banji motsinsu ba"?. Kai prince Hamid ya d'aga "eh Abba suna can". "Ok shikenan Ahmad kai kuma zan dawo gareka" yana fad'in haka ya mi'ke momy ta rufa masa baya zuwa rakiya ina motocin dukkan masarautar suke. Ganin saura su biyu yasa Ahmad ya hade rai yana cewa. "Meyasa zakai min haka gashi yanzu ka jefa ni cikin risky". Ta'be masa baki prince Hamid yai yana cewa "Ba wani risky dana saka ka meyasa kaima ka kasa yiwa Abban bayani saboda ka daki 'yar lelen shi da ya sani da kaima ka samu rabon ka". 'kara hade rai Ahmed ya kuma yi "oh wanne irin rabo kenan zan samu"?.. "Kafi d'an dako sanin tasha saidai ya fika d'aukar kaya Allah yasa babyn su had'u da Abba koda a gurin Sultan Ameer ne aikaga asirin ka ya tonu abinda kake 6oyewa Abban zai gani ko bata fad'a Ahmad saina fad'a ko baka so kai mugu ne na ajin 'karshe". Mi'kewa Ahmad yai zai fita yace "ai baka sani ba Abdul-hamid Aliyudeen Sharfaddeen isa nai muguntar ma iyawa ce idan wani ya isa shima yayi" yana fad'in haka ya fita a parlon d'aga murya prince Hamid yai yadda Ahmad d'in zai jiyoshi yana cewa. "Zakaga mugunta iyawa ce wallhi so kake nasa a hanaka yarinyar nan in nuna maka qarshen mugu haba mutum sai zalunci da zafin rai kamar wani wuta kodan dama haka ka tashi tun kana yaro 'ya'yan bayi ma sunci duka hali ne a jikin rai tunda haka kake bazaka ta'ba canzuwa ba" shima prince Hamid d'in mi'kewa yai da lap Cort a hannunsa ya fita a parlon. Mami tana zaune Sultan yana kusa da ita kuma dama shagwa'ba yake mata ganin Ahmad ya shigo yasa yai sauri shiga hankalin sa yana daidaita kansa yace. "Good morning yaya"?. Zama Ahmad yai yana kallon sa batare daya amsa ba yace "uban me kakewa shagwa'ba"?. 'Dan zaro ido Sultan yai yana soshe soshe yace "uhmm uhmm". "Uhmmm me bana son shashanci so kake yanzun nan jikinka yai tsami Mami miyake nema bai tafi school ba sai lokaci ya fita". Murmushi Mami tai tana cewa "waifa jiya ne ya tafi da tart makaranta yaji dad'in sa shine yace yauma saiya tafi dashi nace masa ba kamar indomie ne ko meat pie da za'ayi a rana daya baya amma ya d'age sai shagwa'ba yake zubawa harda shura qafa kodan yaga ya girma baida qani ne oho masa" Mami ta qarasa maganar tana shafa gashin kan Sultan wanda yai wuqi-wuqi yana d'an satar kallon Ahmad daya had'e rai yana cewa. "Oh har yanzu bakai hankalin da za'a fad'a maka magana kaji ba tunda bazai yuwu a yau ba why not ka ha'kura zuwa gobe ko wani abu zai haifar ma idan baka ciba"?. Shiru Sultan yai ya kasa cewa komai sai addu'a da yake Allah yasa kar hakan dayai ya zama laifi "get lost" yaji muryar Ahmad aiko da sauri ya mi'ke kamar zai kifa yai hanyar fita dakatar dashi Mami tai. "Sultan dawo ka manta plantain mosa d'in naka ko ka fasa tafiya dashi"? Eh kawai Sultan yace sama sama bai tsaya ba hai yake ya fice saboda tsoron karma ya tsaya ya jawa kansa laifi tunda Ahmad yazo. "Kaii dawo ka d'auka". Cak ya tsaya waje daya cikin firgice ya juyo yana kallon Ahmad muryarsa ya kasa fita balle ya iya furta kalmar ya fasa tafiya dashi...................... "Me kake kallo ne dawo ka d'auka nace kada ka bari in tashi a kanka". Jin abinda Ahmad yace yasa da sauri Sultan ya dawo yana ra'be ra'be ya matso a hankali yana kallon Ahmad dan abun na kusa da dashi gani yake idan yazo d'auka zai rikeshi da 'yar sand'a ya yasa hannu ya d'auka da gudu kuwa ya juya faaaaaaaa🏃🤣 ya fice daga part d'in wanda yasa dole Mami tai dariya ai dama Ahmad d'in ne daidai dasu tunda prince Hamid bamai zafi bane Shadat ne d'an uwan Ahmad kuma baya nan sai ranar daya dawo shima haka yake da zafin rai.............................. Hankalin Ahmad ya mayar kan Mami yana cewa "barka da safiya Mami fatan kin tashi lafiya"?. Har lokacin fuskar Mami da fara'a tace "lafiya qalau na tashi Ahmad ya kake ya gajiyar zama wuri daya dan nasan yanzu a takure kuke ku sojoji kun saba rai da rai kuna tsinka jinin jiki idan kunzo hutu kuma ba wani abu zakuyi ba duk sai kuji ku a takure". Murmushi Ahmad yai yana kallon ta yace "ai Mami duk wanda ya saba da aikin ko zaman awa biyu yai batare da yayi wani abu dazai motsa jikinsa ba duk sai yaji babu dad'i shiyasa na dau qaramin hutu da wuri zan koma". "To Allah ya taimaka Ahmad Allah ya fitar daku aikin nan lafiya". "Amin Mami ina baby da khairat ko ba anan suka kwana ba"?. "Kaita d'aga "eh anan suka kwana domin da asuba na buga musu qofa su tashi suyi sallah kuma ko sun tashin Allahu a'alam inaga barci suka koma". "Ok" Kawai yace yana mi'kewa yai hanyar bedroom d'in a qanqame yaji qofar sun saqace ta taciki bugawa yai da qarfi batare dayai magana ba jin shiru babu ko motsi yasa ya qara bugawa still baiyi magana ba juyi Khairat tai tana jan tsaki ta sake sabon kwanciya daidai an qara bugu mai qarfi fiya dana baya a hasale ta tashi zaune tana cewa. "Sultan dallacan meye haka idan baka bar bakin kofar nan ba saina fasa maka baki idan ka bari na fito banza kawai". Jin abinda tace yasa Ahmad ya jinjina kai yana cewa "Ok fito ki fasa min bakin, zaki bud'e ko saina 6alle murfin kofar na shigo naci ubanku ashe dama barci kuke baku tafi school ba yau sai jikinku ya fad'a muku". Zaro ido waje khairat tai cike da tsoro domin yanzun kam ta fahimci waye d'ora hannu tayi aka tana cewa "nashiga uku dama ya Ahmad ne jin ya sake bugawa yana daka tsawa yasa a firgice tace "baby baby tashi yau za'ai farfesun mu yau mun kad'e har ganyen mu" ta qarasa maganar tana girgiza Baby wacce ke barcin ta hankali kwance batasan meyake faruwa ba jijjiga ta tayi da qarfi tana cewa. "Baby ki tashi dan Allah masifa cefa ta tunkaro mu wacce bamu da maganinta sai Allah ba lallai muga gobe ba". Bud'e ido Baby tai cikin muryar barci tace "Aunty Khairat lafiya kike tashi na"?. "Inafa lafiya Baby ya Ahmad ne yake buga mana kofa yanzu na d'auka Sultan ne nace zan fasa masa baki yace na fito na fasa masa yana jirana". Jin abinda Khairat tace yasa Baby tai cilli da bargon data lullu'ba gefe tana tashi zaune a rud'e zatai magana suka ji qarar 6alle kofa kafin su farga sai gani sukai murfin ya fad'o ciki, cikin 6acin rai Ahmad ya shigo zabura sukai a gigice musamman Baby da bata warke daga dukan dayai mata jiya ba tsayawa yai a bakin kofa yana kallonsu su gama iskancin rud'ewar yana daidai dasu ganin sun rikice sosai yasa ya buga musu tsawa....... "Uban me ya hanaku zuwa school yau, raini ko"?. Da sauri khairat ta girgiza kai tana cewa "wallahi ya Ahmad a'a ni bani da lecture da safe sai karfe uku zan tafi". Maida da kallonsa kan baby yayi wacce ta gama haukacewa domin ita bata da hujjar kin zuwa yace "ke kuma fa uban me kika tsaya yi baki tafi ba". Kuka kawai baby ta saki na tsantsan tsoro jikinta sai rawa yake ta kasa magana cikin tsawa yace "uban me ya hanaki zuwa school yau baby"?. Yana rufe baki ta d'ora hannu aka a gigice tace "yaya wallahi bana jin dad'i ne da zazza'bi na kwana". Wani kallo ya mata tare da jinjina kai yace "ku biyo ni" juyawa yai yana fita a rud'e suka mi'ke suna bin bayansa Mami dake zaune Ahmad yazo zai fita yana cewa "ki huta lafiya Mami". "Ok Ahmad nagode sai anjima" ta karasa maganar tana binsu khairat da kallo Wanda babu me cikekken nutsuwa a cikinsu hum tasan za'ai haka dama tunda naji qarar 6alle kofa tasan basu suka tashi suka bud'e masa kofa ba karyawa yai ya shiga aiko yau sun shiga uku. Yana tafe suna binsa a baya har part d'insa yana shiga ya wuce bedroom ya barsu a falo kowa hankalinta a tashe sun dad'e bai fito ba harsun d'auka ma koya manta dasu ne can suka sake jin qarar bud'e kofa ya fito yana gyara allura zaro ido baby tai a firgice tana fad'in innalillahi badai ita zaiwa allura ba............. "Ke zomin nan" taji muryarsa a susuce ta fara zubar da hawaye kuma ta kasa d'aga qafarta balle taje. "Baby kada ki bari na tashi a kanki"?. Jiki na 6ari ta fara takows zuwa inda yake kafin ta sake ja ta tsaya tana kuka tace "dan girman Allah ya Ahmad kayi ha'kuri" tana rufe baki ya mi'ke yana tasowa inda take aguje ta juya zata fice ya dam'kota yana matseta a jikinsa da yadda ko motsi batai masa sannan ya juyata yayi mata allurar humm tsabar tsananin kuka daya ci qarfinta har shid'ewa take wulli yayi da sirinjin yana zama akan kujera ya d'ora kafa d'aya kan d'aya yana kallon ta yace. "Can you be quiet or not"?. "Idan baki rufa min baki ba na tashi sai jikinki ya fashe tsabar duka". Jin abinda yace yasa dole da sauri ta had'iye kukanta tana na zuci kallon Kharat wacce ke qame guri d'aya yayi yana cewa "ba baki da lecture ba? Sai qarfe uku kince, saiki wuni zuwa Nan da qarfe ukun kina karbar hukunci kinga gaba ranar da baki da lecture bakiyi barci ba saiki dau littafi kiyi karatu fara frog jump" yana rufe baki da sauri khairat ta ri'ke kunne ta fara zaga falon wani kallo yaiwa baby yana cewa "ke me kike jira, ko allurar batai miki ba zazza'bin bai sauka ba" jin abinda yake fad'a yasa baby da sauri ta girgiza masa. "Ok fara up and down". Innalillahi up and down kuma nashiga uku yaya kashe ni yake son yi............ "Tunanin uban me kikeyi". Baby batai aune ba taji saukar duka a bayanta a hargitse ta fara abinda yace mata yana zaune yana kallon su kowa kuka take tsabar wuya gashi babu damar d'an tsayawa su huta daga wannan su koma wannan iya gala'baita sunyi saida ya tabbatar yadda jikinsu zai fad'a musu sannan yace su tsaya haka tsayawa sukai da'kyar suke iya jawo numfashinsu kai ya jinjina yana cewa. "Get to the point gobe ma ku kwanta kuyi barcin safen Ina daidai daku get of my sight" yana rufe baki har gware suke waje gudun fita kowa jan qafa take musamman baby da bata da lafiya har juwa ke dibanta suna shiga parlon Momy kuwa ta yanke jiki ta fad'i qasa bata ko motsi subahanallahi da sauri khairat ta dur'kusa tana jijjiga ta daidai Momy ta fito tace. "Innalillahi khairat meya samu babyn kuma yakai ta fad'i"?. A rikice Khairat tace "Momy baby bata da lafiya da zazza'bi ta kwana dan Allah ki kira ya Hamid yazo ya dubata". "Hamid ya tafi hospital bari naje Ahmad ya kirashi waya na network d'inta ya sauka " Momy ta fad'a tana ficewa mi'kewa Khairat tai ta nufi frigde zata d'auko ruwa ta shafawa babyn amma me itama tana mi'kewa juwa ta debeta ta fad'i a gurin, tare da Ahmad Momy suka shigo ganin itama Khairat d'in ta fad'i yasa hankali tashe Momy tace. "Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un meye yake damunsu ne kodai sunci wani abu me guba ne"?. Shiru Ahmad yai ya zuba musu ido yayin ta Momy ta shiga kai komo a parlon hankalinta inyayi dubu ya tashi har Hamid ya shigo Shima dai babu nutsuwa a tare dashi ganin ba iya baby bace harda Khairat yasa mamki ya rufe shi yana kallon Momy yace. "Meya faru dasu haka suka fad'i a lokaci guda". Kai Momy ta girgiza tana cewa "ban sani ba Hamid bansan meke damunsu ba kawai ka dubasu" Momy ta karasa maganar daidai wasu bayi masu ayyuka a part d'in sun shigo ta umarcesu dasu shiga bedroom d'in Khairat su ciro katifar dake kan bed d'in su kawo mata ita parlor, amsawa sukai kamar ta basu umarni suka d'auko suna kawowa Hamid ne ya taimakawa Momy ta dorasu akan katifar sannan tana tsaye tace ya dubasu, hum yayi mamaki baby zazza'bi take kuma a gwajin dayai Mata ya sauka to amma Khairat fa baiga komai ba saidai gaskiya dika su biyun suna bu'katar a qara musu ruwa, kallon Ahmad yai wanda ya had'e rai kafin ya jinjina kai yana d'aurawa kowaccensu drip a hannunta da zaiyiwa Momy wata magana amma sakamakon da Ahmad a gurin kuma zasu iya yin hayaniya yasa kawai ya share daya kammala abinda dazai musu ya koma hospital yace idan ya dawo zaiyi magana da Momyn, Ahmad ma bai zauna ba ya fita sai iya Momy ce a gurin su ta d'auko bargo tana rufesu domin sunyi barci. 'Dorayi^^^^ ____Tafe wata budurwa take ita kad'ai ko ganin inda take jefa qafarta batayi saboda irin damuwa da tunanin datai zurfi a cikinsa ga kuma hawaye yana zuba na ba'kin ciki da takaicin rayuwar gidansu da halayyar yan gidan musanman matar ubanta da kuma shi kansa mahaifin nata wani lokacin har tunani take anya shine ya haifeta ba tsintar ta yayi ba uba na qwarai bazai ri'ka cutar da yarsa irin haka ace ba kula ba walwala ba nuna qauna magana ta fatar baka wacce zatasa taji dad'i bazai Mata ba ya'ki mayar da hankali akan iliminta amma yake biyawa su Abidah da Nadiya bashine ya haifesu ba ita da take 'yar hatta kud'in da zata hau napep baya bata kullum a qafa take zuwa makaranta amma su Abidah kwanan nan ya sauya musu mota ta zuwa school........ kuka ne me qarfi taji yana tunkaro ta cikin dauriya ta danne taci gaba da tafiya ga masifar gajiya datai ga yunwa kuma ta tabbata saita koma zata d'ora musu girki ta gama ta dauko ta kawo musu dining tai serving kowa kamar wata bewar su suyi kaca-kaca da dinning din ita zata gyara ta tattare kwanuka ta wanke ga su sata wanki suna zaginta da injin wanki a gidan amma tsabar sun karanci mugunta ruwan da zatai musu wankin ma sai sun zuba Mata qanqara d'uma d'uma a ciki yadda hannunta zai sanqare haka zasu tulo Mata kaya ta wuni a tsakiyar rana tana wankewa su bushe ta goge ta kaiwa kowa cikin wardrobe dinta abin nan yana mugun ba'kanta Mata rai rashin uwa maraici yaja Mata haka da ace mahaifiyar ta tana nan bazata tozarta haka ba share hawaye tai har ta kusa ta tuna littafinta ta mantoshi akan kujera cikin class da sauri ta juya zuwa FCE d'in batare data tuna cewa hakan zai zama Mata laifi bane a gurin Hajiya Khuburah gashi kuma data koma bata ganshi ba sannan babu students ko d'aya balle ta tambaye su ha'kura tai cikin damuwa ta sake d'auko hanya ta dawo gida tana bud'e gate d'in gidan saida gabanta ya fad'i ganin motar Daddynta ya akai yau ya dawo da wuri bayan kullum sai magriba yake dawowa gida yau kuma tun la'asar shiga tayi jiki a sanyaye ta bud'e kofar falo da sallama shiru kamar ba mutane babu wanda ya amsa Mata sai tu'kuicin baka'ken harara data samu kaita sunkuyar zata wuce cikin tsawa hanya Khuburah tace. "Zo nan dan uwarki". Jin abinda hajiya Khuburah tace yasa ta dakata tare da juyowa ta dawo har gabanta ta dur'kusa tana cewa. "gani Mama''. Wani irin kallo tayi mata cike da tsana tana cewa "a gidan ubanwa kika tsaya sai yanzu kika dawo ana jiranki kizo ki d'ora girki tsabar ba'kin hali shine kika tsaya a wani wuri baki zo akan lokaci ba bayan kinsan Nadiya tana da ulcer bata juri zama da yunwa ba amma kika kama kika zauna a hanya ko, a gidan ubanki kika tsaya"? ta karasa maganar tana kai mata mari, hawaye ne masu zafi suka shiga zubowa Ayrah wato ita da yake bata da wanda zai tambaye ta taci ko bataci ba uwa balle ta samu kulawa a yau banda biscuit da drinks data sha a gurin qawarta Zarah bataci komai ba domin datayi musu kayan breakfast hajiya Khuburah cewa tai ta 6ace mata da gani haka ta tafi school amma ga wacce kawai dan batazo ta d'ora girki da wuri ba har ake zaginta............... Ba zato taji sun rufeta da duka kamar zasu kashe ta sai tattaka ta suke hajiya Khubura tana zaune a hakimce ta d'ora qafa d'aya kan d'aya sai kad'a kai take tana cewa "kuci uban daya kawota duniya sawa tace ku fasa Mata baki". A fusace Nadiya dake faman d'irkarta ita da Abidah tace "anya mum wannan da ba dabba za'ai yi bata akai mutum kwata kwata ace yarinya ta zama me dod'add'iya qwaqwalwa duk abinda aka fad'a Mata bazai shiga kunnen taba saikace jaka"?. Ta'be baki hajiya khubura tai tana cewa "da alama dai jakar ce domin bata sahun mutane a gurina dan naga qwaqwalwar jakuna gareta dukan da kuka lakad'a Mata bai shigeta ba shiyasa ta tsaya kuka kuci gaba da nad'ar 'yar isa sawa tace ku fasa mata baki" hajiya Khubura ta karasa maganar tana hankad'a Ayrah baya tare dasa qafa taka Mata ciki, qara Ayrah tai cike da azaba a take wani wahalallan amai ya fara fito Mata har ta hanci, da sauri hajiya Khubura ta matsa gefe tana sa hannu ta kare hanci da baki wai karta d'auki cuta tace. "Kan uba mu zakiwa qazanta a parlor gurin zama da hutun mu aiko saikin shanye sa😳". Kuka Ayrah keye sosai cikin damuwa hannuwanta a bud'e alamar neman yafiyarsu muryarta na rawa tace "dan girman Allah Mama kiyi hakuri zan gyara gurin". Cikin tsawa hajiya Khubura tace "karki kuskura ki sake kirana mama domin ni ban haifi 'ya asararriya irinki ba kije can qabari ki nemi uwarki Allah ya sauwa'ke na miki kallon 'ya hayyy tabdijan amma baki ma da hankali Wallahi daga yau na sake jin wannan tsinannan bakin naki ya kirani da Mama saina kusan kashe ki a gidan nan kuma kiyi abinda nasaki ki shanye wannan aman" ta fad'a tana kifata a gaban wuri tace. "Abidah ni ta raina min wayo kuzo kusata ta shanye wannan qazantan data zubar mana". Tasowa sukai Nadiya ce akan gaba tana zuwa ta d'auke ta mari zatai magana itama taji saukar wani irin firgitaccen mari me tafiya da ji da gani ya sauka a fuska kafin ta wani yunkuri sabo wanda yafi na farko ya sake sauka a daya 'barin a gigice Nadiya ta fasa qara wata ba'kar juwa ta debeta tayi baya timm ta fadi kasan carpet tana fashewa da kuka wanda kafin su farga cikin zafin nama Abidah ma ta samu nata rabon itakam da yake tafi Nadiya raki ihu tai ta zundumawa tana burgima a kan carpet d'in kamar ana yankar jikinta. Yana tsaye a kansu ransa a mugun'bace idonsa yayi ja kallon yadda jikin Ayrah ke rawa yayi takaici na sake rufeshi kamar ya cire belt din jikinsa ya musu shegen duka yake ji sai kuma ya fasa dukawa yayi yana d'ago Ayrah batare da yace mata komai ba sai mahaifiyarta da yake tunawa irin ri'kon datai masa kamar d'an data haifa idan ya zuba ido akaci gaba da cutar da yarinyar nan bazai ta'ba yafewa kansa ba............... Katse masa tunani hajiya Khubura tai sakamakon wata ba'kar d'anyar ashar data danna tana cewa "Aiman ka fita idona a cikin gidan nan ina ruwanka da lamarin mu na rantse da Allah bazan yarda bari Alhaji ya fito ya mana iyaka domin wallahi saidai ka koma gidan ku ko kuma ni ya sakeni na bar masa gidansa bazanci gaba da zama kana nuna min rashin tarbiyya irin wacce Fatima ta koya maka ba kasan laifin da tai min kawai zaka dau hukunci a hannunka wato kaiga isashshe d'an isassu me qanwa ko''?.. (Fatima mahaifiyar Ayrah ce ta rasu shekaru uku da suka wuce itace ta reni Aiman shi d'an qanin Daddyn Ayrah ne tun daga yaye ya'ki gidansu yake zaune a gurin Fatima komai nasa kuma tamkar uwa haka ta daukeshi sannan ta raineeshi a matsayin nata). Wani irin razanannan kallo me firgitarwa Aiman yayi mata wanda yasa cikin shakka ta soma matsawa baya baya tana cewa "wallhi bari kaji tunda juninka fitsara zan gwada maka Nima ba kanwar lasa bace zanje gidan naku zan hadaka da wadanda suka isa dakai suyi min maganinka Ina daidai dakai d'an marar kunya kawai". Nunata Aiman yayi da yatsa a fusace yace "karki sake zagina kin gane"?. Itama a fusace tace ''na zaga ubanka ya buge uwarka tsinanne la'ananne ni zakaiwa rashin da'a? To bari kaji ko Zainab uwar data haifeka bata isa fad'i in fad'a Dani ba balle wani banza kai data haif............. Bata karasa ba ya wanketa da mari ihu ta zunduma daidai Daddy ya fito baiga sanda yai Marin ba ihunta kawai yaji gasu Abidah da Nadiya har lokacin suma suna kukan zafin da fuskokinsu ke musu da sauri ya karaso yana kallon Aiman yace. "Subahanallahi me yake faruwa Aiman ya naga haka kukan me suke"?. Tun kafin Aiman yai magana hajiya Khubura dake ri'ke da kunci cike da takaici tace "au Alhaji shi zaka tambaya bayan wulakanci da cin mutumcin dayai min marina fa yayi". "Mari dai"?. Daddy ya tambaya cikin mamaki yana kallon ta da alamar rashin yarda akan abinda ta fad'a, haushi ne ya rufe hajiya Khubura a fusace tace "eh mari yanzun nan ya mareni akan nayi masa magana ya mari Abidah da Nadiya". Kallon Aiman Daddy yayi yana cewa "meyasa ka maresu Aiman me sukai maka"?. "Daddy Ayrah suka saka a gaba suna dukanta kamar zasu hallaka ta harda amai kalli inda tai kuma tsabar rashin imani wai saita shanye, wacce irin rayuwa ce wannan suzo suna qarqashin inuwar mahaifin ta suna cutar da ita komai itace take musu hakan bai ishesu ba sai suna dukanta to wallahi bazan yi lamani ba" ya karasa maganar yana hararar su Nadiya dake gefe suna jan ajiyar zuciya. Shiru Daddy yai ya tsume yana kallon Ayrah jin a kanta ne komai ya faru kuma Aiman harda marar masa mata nunata yayi da yatsa yana cewa "wato ke kin zama shed'aniya ko? Kullum sai an samu sa6ani a gidan nan a kanki kin hana zaman lafiya to bari kiji idan har baki gyara ba sai na dauki mummunan mataki a kanki zan bayar dake". Daddy na rufe baki Aiman yace "Daddy ba laifin Ayrah ga babbar me lefi nan Hajiya Khubura itace ta gur6ata zaman gidan nan ba kowa ba da a lokacin da Umma tana raye ai ba haka muke zaune ba bamusan rayuwar 'kunci ba sai sanadin shigowarsu cikin rayuwarmu dan haka Ayrah tana gidan insha Allahu babu inda wadannan agololin zasu sa taje". Mi'kewa Hajiya Khubura tai tana cewa "idan Kaine ka haifeta saika hana ya sadakar da ita me gida yace bazata zauna masa a gida ba kaga ko kai dan karere baka isa ka hana ba dole ta hada kaya ta kama gabanta". "Wallahi babu inda Ayrah zataje tana gidan nan tunda gidan mahaifin tane saidai su koma gidan ubansu". A masife Hajiya Khubura tace "kaine zaka koma gidan ubanka tunda ai kaima zilama ce ta dawo dakai nan d'in ai kasan yafi mahaifin ka kud'i idan ba tsoro ba ka koma". "Look malam don't disturbing me ba dake nake ba da mahaifina nake dan haka ki rufa min baki kin gane"?. "Bazan rufe bakin ba kad'au mataki d'an me ido a tsakar ka mara mutunci kawai". "Na fada miki da ki daina zagina wallahi tallahi daga Rana irin tayau idan kika kuskura tsautsayi yasa kika sake zagina, humm na rantse da Allah saina 6allaki a gidan nan tunda ke ba uwa ta gari bace". Zainab ce ba uwa ta gari ba amma dai bani ba idan ka fasa 6allani kai ba d'an halak ban............ Bata karasa ba tayi shiru tana matsawa baya da sauri harta kusa fad'uwa qasa sakamakon hannu daya d'aga zai sake kifeta da mari a karo na biyu maganar Daddy ce ta dakatar dashi daga yunkurin sa. "A'a Aiman bari kada ka sake marinta". Huci me zafi Aiman ya fitar yana sauke hannunsa qasa tare da doka Mata wata uwar harara yaja tsuka cike da fusata ya fice daga parlon ran hajiya Khubura na quna ganin yadda yaci Mata fuska a gaban 'ya'yanta amma Daddy baice masa komai ba bai nuna masa 6acin rai ba yasa taja qaqqarfan tsaki tana kallon su Nadiya tace. "Ku tashi kuje kuyi wanka muje eateries muci abinci acan tunda wannan d'an iskan yaron ya gama 6ata min rai yau bazai bari tayi mana girki a gidan nan ba idan tayi ma zai iya lalatashi ko yasaka mana guba a ciki muci mu mutu ba damuwar sa bace dan naga d'anye ne". Mi'kewa su Abidah sukai suna shiga part d'in su hajiya Khubura zata bi bayansu saida ta bangaje Ayrah harta fadi ta baya ta take Mata yatsun hannu tana cewa "ubanki kike kallo a jikina mayya kika zuba min wandannan tsinannun idanuwan naki aikin banza uban me za'ai da auren mutum me d'a a hakan ma d'an kishiya" ta qasara maganar tana kallon Daddy daya d'ago suka had'a ido kafin fuuu ta bud'e kofa ta fice shiru parlon yayi na wani lokaci Daddy ya zubawa Ayrah ido so yake yayi tunani akan wani abu game da ita ya kasa tuna komai yasan Ayrah 'yarsa ce kuma hakan bai 6ace masa ba amma a ransa yana jin wata iriyar ba'kar qiyayyar ta ko ganinta bai so wanda ada yasan ba haka bane to meya sameshi ne, qara zuba mata ido yayi tana dur'kushe a gurin da hajiya Khubura ta kifata kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa ya nufi hanyar fita saboda an kusa kiran sallar magriba Ayrah tana kallon Daddy ya bud'e kofa ya fita wani irin zazzafan hawaye ne me d'aci yake fita daga idanuwanta ta sani mahaifin ta yana matukar sonta kafin rasuwar mahaifiyarta da kuma bayan rasuwarta yana tausaya mata dalilin haka yasa ya'ki aure da farko saboda yana tsoron irin matar da zai yayowa kansa irin muguwar matar dazata shiga tsakanin sa da 'yar shekara biyu da rasuwar mahaifiyar Ayrah ya kasa yin aure yace saiya samu mace mai d'a wacce tasan dad'in d'a zata ri'ke masa Ayrah tsananin ta da Allah ta bata gata ta yaye Mata kewar uwa data rasa amma baiyi dace ba ya auri hajiya Khubura Mai 'ya'ya uku domin tana d'a saurayi yana can qasar rasha (Russia) yana karatu sunan sa Khalil bai ta'ba zuwa gida ba tunda tai sabon aure shekara guda bayan rasuwar mahaifinsu. Mi'kewa Ayrah tai jikinta yana Mata mugun ciwo sakamakon dukan dasu Nadiya sukai mata har jan qafa take ta shiga part d'in mahaifiyar ta inda yanzu a ciki take rayuwa da komai nata tun bayan auren hajiya Khubura da Daddy yai tamai asiri tare da kad'ar masa hankali akan ayrah tun daga lokacin komai ya fara sauyawa rayuwar qasqanci ta sameta kamar ba gidan mahaifin taba ko yar aiki bazata fad'a mata bautuwa a gidan ba hatta bedroom d'inta su Abidah sun koreta sune suke kwana dole sai part d'in mahaifiyar ta takoma. MRS ÃL'ÅMÉÉÑ ÁHMÃD CË. Tnks for your supports🔥. Naja'at Musa Abubakar Fatima Musa Abubakar Salim Musa Abubakar Aisha Musa Abubakar Abubakar Musa Abubakar Everything about you is so good but one thing is wrong that you are not mind. We will meet again. TYPING📲 Mon, Nov,11/24 11:06AM YUSRAH MUSA ABUBAKAR💋🤟. 👑ROYALTY👑 ÀÑÑÙRÌ WRITER'S ASSOCIATION 💫 Home of hospitality and harmony gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan ta. WHATSAPP no:234 816 098 3083. DEDICATED TO My daughter Fatima Zarah (Ilham). STÔRY WRITTEN ND EDITING YUSRAH MÛSÃ ABUBAKAR Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë. ___________________ _____________________________ ____________________________________ 2~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Mujahidina. @YUSRAHMS CE Page 03 & 04 👑PALACE👑 Yau tun bayan sallar asuba baby batai marmarin sake kwanciya ba wanka tai ta shirya tun lokacin school baiyi ba bata tsaya zancen breakfast ba kawai ta dauki Jakarta ta fito a part d'insu ta shiga part d'in Momy bata lura da Ahmad ba sai da taji yana waya da sauri ta juya ganin irin kallon da yake aiko Mata yasa kawai da tacewa prince Hamid good morning dan karta tsaya ya gama waya ma ya qaqalo Mata wani abun lefin yasa ta juya zata fita kai Ahmad ya jinjina yana mikewa ya fita ta dayar kofar batai zato ba sai ganinsa tai a gabanta da sauri tayo baya tana zaro ido me kuma tai masa zai tare ta........... Katse Mata tunanin yai ta hanyar jawota yana kallon prince Hamid daya biyo bayan Babyn yaga me Ahmad d'in zaiyi mata domin yana kallon lokacin daya jinjina kai shiyasa ma ya taso saboda karya cuceta sakar masa hararar gargadin ya sake ta yayi amma kamar Ahmad bai gani ba ya d'auke kai yana dawo da kallonsa kan Baby yace. "Which rubbish is this"?. Da mamaki tace "me nayi yaya"?. "Oh tambaya na kike¿ Do you want to know why? Na miki tambaya kema kina tambaya na? Da wannan d'an hijab din zakije school are you out of your sense "?. Wani kala tai da fuskarta tana kallon shi innalillahi yanzu tsakani da Allah mene laifin wannan hijab d'in dama talhat ai haka yake nata ma yana da girma akan na wasu........... "what are you looking😕"?. Taji ya sake jefo Mata tambaya d'ora hannu tai aka gaskiya ya Ahmed bazai ta'ba barin ta tai 'kiba a gidan nan ba yanzu meye aibun wannan hijab d'in dan kawai tayi kuskure a magana ya nad'eta shiyasa yake mata irin wannan tambayar...................... "Baby". "Na'am yaya". "Kina son ganin fushi na ko"?. "A'a yaya". "To amma meyasa duk abinda kikasan bana so ke kuma shi kikeyi ban hanaku saka irin wadannan hijab d'in ba"?. "Ka hana mu dan Allah kayi hakuri yaya bazan sake saka irinsa ba bari na sauyo wani yanxu" ta fad'a tana juyawa zata koma part d'insu a bisa tsautsayi ta buga 'kafar ta jikin qofa qara ta saki tana dur'kusawa a gun cike da azaba ta dafe gurin data bugun kafin ta d'ago tana kallon Ahmad taga shima ita yake kallo jin saukar muryar sa tai yace. "What"?. Fad'in hakan yasa taji idonta ya cika da hawaye maida hankalin sa yai kan qafar ganin yadda take matsa yatsan data bige yasa yasan taji ciwo ne matsawa yai kusa da ita domin ya duba mata amma saita d'an matsa daga gareshi a razane gira ya d'auke yana cewa. "Oh is like you don't need my help right"?. Batai magana ba prince Hamid dake tsaye a d'an nisa dasu shine ya matso yana cewa "eh bata buqatar taimakon naka malam zaka iya fecewa dama ai bakai niyyar ka taimaka mata d'in ba bayan silarka ne ta buge". Ta'be baki Ahmad yai jin abinda prince Hamid d'in yace yana gyara tsaiwarsa ganin ya kusa karasowa yasa Ahmad ya kama qafar babyn ya matsa ta da kyau qara tai tana kuka kafin ya jinjina kai yana ficewa d'aga murya prince Hamid yai yana cewa "kaji kunya dai wallahi Ahmad kaji jiki babu 'yan dubiya haba ayi mutum muguntarsa tafi qarfinsa kai gani kake hakan ado ne ko humm d'an rainin hankalin yaro zan had'aka da Abba tunda shi ya isa dakai yayi maka magana abun ya isa haka" ya karasa maganar yana d'agota daga dur'kushen da take yace "kinga baby rabu dashi kiyi ha'kuri kinji Ahmad baida hankali kina hattara dashi karki ri'ka shiga safgarsa tunda baki laifi bama zaluntarki yake balle ki masa wani abu ya samu mafaka muje na mayar dake part d'in Mami ko gurin Momy zakije ki ha'kura da zuwa makarantar yau naga kamar qafan na miki ciwo sosai ko"?. Kai baby ta girgiza tana d'an yarfa hannu tace "a'a ya Hamid ina son zuwa school yau akwai wani programs da za'ayi kuma harda ni a ciki sannan muna da test na biology zamu shiga qarfe sha d'aya da rabi dole naje zan iya zuwa ka rakani gun driver ya kaini" Kai ya d'aga mata yana cewa "ok baby karki damu muje da kaina zan kaiki tashi mu tafi kada kiyi late" mi'kewa tai daidai tana d'an d'ingisa qafar suka fita khairat ce bata da lacture sai qarfe hud'u na yamma dan haka batasan wainar da ake toyawa ba tana bedroom tana hutawa abinta har cikin school prince Hamid ya kaita tare da shopping na kayan cinye cinye daya saya mata tayi ta masa godiya dan tasan abinda Ahmad bazai ba kenan wai yau ace rana ce ta fito ya rakota makaranta yana lallashinta harda yi mata sayayya hum'um ranar da anyi ruwan sama mai qanqara tasan abu d'aya ne ko zai kawota saiya gwangwaje ta bazai kawota a banza ba baya aikin kawai. Suna zaune tare da qawarta Ayrah bayan tafiyar prince Hamid fitowarsu kenan daga gurin da akai programs d'in kafin a shiga musu test duk da lokaci ya kusa saura 'yan mintuna kallonta Ayrah tai tana cewa. "Zuhra Ashraf Sharfaddeen ya akai ne yau waye gayen daya kawo ki school ai na ganshi ko brother d'in kine naso zuwa gurin amma da naga ba driver daya saba kawo ki bane shiyasa na fasa na juyo nayi tunanin ko kin ganni amma sai naji baki magana ba shiyasa ma na tambaye ki"? Murmushi baby tai tana cewa "meyasa kika tambayi waye shi"?. "Babu kawai dai na tambaya ne" cikin tsokana baby ta girgiza kai tana cewa "um um fa Ayrah fad'i gaskiyar ki naji". Hade rai Ayrah tai tana cewa "um um me"? Ta fad'a tana kallon babyn ganin dariya take mata yasa ta zaro ido waje tana rufe baki tace "ke Ashraf Sharfa karfa kimin fassara ba wani abu nake nufi ba dan na tambaye ki". "Oh to kuma nima ai bakiji nace wani abu ba ko na daiyi mamaki ne da naga kin dage kina tambaya a kansa". "Ok kenan ba'a tambayar waye shi ko nayi laifi kenan"?. "A'a no dan kawai kin tambaya saiya zama abun laifi to ba kowa bane yaya nane sunansa Abdul-hamid". "Wow dama kina da yaya saurayi haka"?. "Eh man gashi kin gani kuma aiba iya shi kad'ai bane su uku ne". "Umm 'kwarai Ashraf Sharfa" kawai shine abinda Ayrah tace tai shiru kamar me tunani sai kuma ta sake kallon Babyn tana cewa "amma shi wanda ya kawoki uwa d'aya uba d'aya kuke dashi"? Kai ta girgiza tace "a'a shi d'an gidan Abba Aliyuddeen Sharfaddeen ne dashi da 'kaninsa ya Ahmad sai kuma Aunty Khairat ni kuma kinga Yaya na baya gida yaje Singapore karatu sunansa Shadad saini da qanina Sultan Sharfaddeen sunan kakan mu yaci". Kai Ayrah ta jinjina tana sake kallon Baby tace "to amma Baby da alama wannan yayan naki daya kawo ki school baida jin kai kamar zaiyi kirki ba irin mutanen nan ne masu shariya ba ko"?. "Eh tabbas wannan haka yake Ayrah Yaya Hamid akwai sauqin hali shiyasa nafi sakewa dashi ba irin su ya Ahmad ba wanda ko barci suke kazo wucewa sai kana sand'a saboda tsoron karya farka su ganka humm boss me zamani kenan dama gashi soja shiyasa zafin ran yai yawa amma ya Hamid so silent ne baida hayaniya ko kad'an". "Gaskiya ne Baby haka nake son mutum ya kasance me faran faran ba wanda kullum fuska tana murtuke a d'aure kamar ta shanu ba". "Ko kema kina da bros me matsa miki lamba ne kamar mu Ayrah"? Kaita girgiza tana cewa "a'a bani dashi nice babba a gurin Daddy na saidai takura Yaya Aiman wani lokacin shima idan yana gidan baya barin mutum ya sake saidai yasaka a gaba kayi ta karatu kamar zaka had'iyi dictionary kafin rasuwar umman mu amma yanzu da Daddy yayi aure gata yake nuna min sosai baya bari na shiga damuwa saidai idan bai sani ba shine yake kula dani". "To shi kuma waye kince kece babba"?. "Eh nice babba Yaya Aiman d'an gidan 'kanin Daddy mune tun daga yaye ya'ki komawa gidansu yake zaune a gidan mu gurin Umma na har gobe ba sosai ma yake zuwa asalin gidan mahaifin saba sai yayi kwana biyu uku baije ba". "Ok ayya Allah sarki Ayrah dama mahaifiyarki ta rasu"? Kaita d'aga a sanyaye tace "ta rasu shekaru uku da suka wuce" kai Baby take girgizawa cikin tausayawa tace "Allah sarki Ayrah sannu Allah yayi mata rahma". "Amin Baby nagode tashi muje kinga an fara shiga maybe lokaci yayi ni saitin agogo na ya goce" ta fad'a tana kallon agogon dake d'aure a hannunta mi'kewa Baby tai tana cewa "ok ni nawa a saice yake idan muka fito saiki gyara nakin muyi sauri wannan lecturer ba kirki ya cika ba shima" wucewa sukai aiko suna shiga ya fara tare kofa yana cewa. "Baku masu taku ba wa zakuyi wa iyayi ni malamin kune ba saurayin ku ba dan haka saiku tsaya idan na rubuta musu sunyi rabi kwa shiga" ya fad'a tare da shigewa ajin yaja kofar ya rufe 'yan matan dake waje sai ta'be baki suke suna kad'a kai domin babu wanda ransa ya 6aci akan abinda lecturer yace dan dama mafi yawansu ba karatu suke ba shashanci kawai suke da samari a makaranta ayo wankan 'kure maki azo makaranta dan a burge samari da malamai koda ace ya barsu ba test d'in zasuyi ba shiyasa ma ya hanasu shiga saboda karsu hana sauran masu niyya su shiga class su dagula musu lissafi,, saida suka gama suka fito sannan yasa suma suka shiga su zana iya su. Su Baby kam gurin da suka tashi nan suka koma Ayrah ta gyara agogonta suka cigaba da hirarsu har lokacin tashi yayi da yake gajeriyar rana ce Ayrah bata tafi ba saboda taji cewa prince Hamid ne zai dawo d'aukar Baby so take taje su gaisa suna tsaye suna zancen su da dariya mota tai parking da mamaki Baby take kallon motar wannan ba motar prince Hamid bace Kuma ba da ita driver yake zuwa d'aukarta ba to waye kodai Aiman yayan Ayrah ne yazo d'aukarta...................... Katse tunanin da take tayi ganin an bud'e kofar da sauri ta d'ago tana kallo taga waye kallon farko fuskar Ahmad ta gani wani irin zaro ido waje tai tana d'an jada baya kad'an ta murje idonta ta sake bud'ewa sai kuma taga prince Hamid ne mamaki ne ya kamata duk da dama suna fusgar kama amma dai yanxu itafa fuskar Ahmad ta gani 'kiri-'kiri kodan tasa tsoron sa a ranta ne?............... "Baby mene ya firgita ki"? Taji muryar prince Hamid da sauri ta dawo daga tunanin da take tana kallon sa ta girgiza kai tana ri'ke hannun Ayrah tare da yin murmushi tace "babu komai Yaya Hamid kawai kallon farko naga ka fito da fuskar Yaya Ahmad ne saida na sake runtse ido na bud'e kuma sai naga fuskarka wallahi Yaya Hamid bakaji yadda zuciyata ta buga ba na d'auka da gaske ya Ahmad d'in ne yazo d'aukata inaga da kafin muje gida sai zazza'bi ya rufe ni". Murmushi ya sakarwa zancen nata yana d'an girgiza kai yace "haba Baby tsoron da kikewa Ahmad ya wuce misali mene abun zazza'bi dan kawai yazo d'aukarki"?. "Uhm ya Hamid dole nayi zazza'bi nasan haka kawai ya Ahmad bazai zo d'aukata ba saidai idan dama akwai abinda ya shirya". "Abun daya shirya kuma? Babu wani abu Baby kawai fa kece kika rud'a kanki dashi tun farko da baki nuna jin tsoron saba da babu abinda zai faru Baby bakisan mene Ahmad yake ji a kanki ba da irin kallon da yake miki da ace zaki fahimce ni dana fad'a miki wani abu dazai baki mamaki wanda ke har gobe baki sani ba amma shikenan dai muje ko" ya fad'a yana nuna mata mota juyawa tai tana kallon Ayrah wacce ke kallon yadda suke magana a sake cike da burgewa murmushi Baby tai mata tana cewa. "Ayrah kizo man ku gaisa ga yayan nawa Yaya abdul-Hamid ya dawo" ta fad'a tana kallon prince Hamid wanda ya kalli Ayrah taci gaba "Ayrah ga Yaya abdul-Hamid ku gaisa" kai Ayrah ta jinjina tana d'an sake fuska tace "ina yini"?. "Lafiya kalau ya karatu"?. "Alhamdulillah" ta fad'a tana kallon Baby wacce tace "Ayrah ki shigo ya fara kaiki gida idan ya sau'ke ki sai mu wuce ko"? Kai Ayrah ta girgiza da sauri jin abinda take fad'a ta sani matukar wani yaga sanda aka sauke ta a cikin su Abidah ko Nadiya wani ya ganta ta shiga uku sharri zasu 'kulla mata a gurin Daddy musamman da yanzu ba goyon bayanta yake ba ya watsar da ita..................... "Ayrah muje man". Baby ta fad'a tana ri'ko hannunta tana janta sake girgiza kai Ayrah tai tare da kankaro murmushin dole tace "a'a Baby nagode karki damu sai ranar Monday insha Allahu" ta fad'a tana sake kokarin daidaita fuskarta dan kada su fahimci komai had'e rai Baby tai tana cewa "ai dama ba ro'ka kikai ba amma a tunani na Ayrah bai kamata dan kawai nace ki shigo muyi dropping d'inki zaki 'ki ba yarda ta dake tafi haka ko"? Shiru Ayrah tai jiki a sanyaye bataso ace sun gane tsoron 'yan gidansu take saboda haka kawai ta ha'kura badan taso ba sai domin karta bar musu kokwanton meyasa ta'ki yarda su kaita gida tun daga nesan gidan tace su sau'keta tsayawa prince Hamid yayi ta sauka tayi musu godiya sosai kuwa domin taji dad'in yadda suka nuna mata kulawa da murmushi akan fuskarta ta bud'e gate d'in ta shiga saidai lokaci guda taji farin cikin nata ya koma ciki sakamakon ganin motar Nadiya data Abidah a parking space kenan suna gida harsun dawo innalillahi wa inna ilaihi raji'un ji take kamar ta juya inama tana da inda zataje da wallahi tabar gidan nan har abada saidai ya zatai da rayuwarta tunda nan ne gidan mahaifin ta haka zataita ha'kuri har karshen wahalar ta yazo tunda karfofi sun zo sun cika musu gida sun fita sakewa da gadara................. Tana shiga parlor ta gansu a zaune kowacce ta d'ora kafa d'aya kan d'aya da waya a hannunta tana shafawa shigarta da sallama yasa suka d'ago suna binta da wani irin ba'kin kallo babu wacce ta amsa mata sai tsawa da Nadiya ta daka Mata tana cewa "ke sokuwa zomin nan" a tsorace Ayrah ta juyo tana kallonta lokaci guda jikinta yad'au rawa ganin ta kasa takowa ta dawo Abidah ta ta'be baki tana cewa "ai baki da isar da zata dawo miki saidai ki tashi kije ki jawo jaka kalli man ki gani tafi 'karfin zuwa haka ne amsar tsaiwarta" ta karasa maganar tana sakarwa Ayrah harara kai Nadiya ta jinjina tana cewa "tabd'ijan aiko yau zataga hauka nice zan tashi naje na jawota saboda Ina so tai min aiki? Hum'um wallahi bazan je inda take ba saita dawo nan har gaba na naci uwarta" dariya Abidah tai tana cewa "ai shikenan bari muga yadda wannan comedyn zai kasance kince itace zata tako tazo miki ita kuma taja ta dake tace bazata zoba mukam yan kallo ne" ta fad'a tana sake gyara zama ciwon yatsa Nadiya tai tana sake daka mata sabuwar tsawa tace. "Zaki zo min nan ko saina ci uwar data haifi uwarki matsiyaciya tinkiya baki gane yaren da nake miki ba saina tashi a kanki"?. Cikin jin takaici da d'acin maganar da Nadiya ta fad'a a kanta Ayrah ta juyo tana dawowa tare da dur'kusawa domin wannan sawar Hajiya Khubura ce tasa indai sukai kiranta tazo ta tsaya musu a tsaye su mata shegen duka tana dur'kusawa Nadiya mi'ke tana danna kanta a 'kasa ta dun'kule hannunta ta tuma mata dundu mai karfi a bayanta tana hankata har saida ta wuntsila kanta ya bugi center table na glass dake tsakiyar parlon da 'kafa Nadiya ta sake taketa tana cewa. "Mi'ke min tsaye bagidajiya wannan ba komai na miki ba cikin ukubar dazan d'and'ana miki tashi ki wuce part d'in mu ki wanke mana hijab dinmu na islamiyya da nikaf kuma wallahi idan basu fita ba sai naci ubanki" ta karasa maganar tana mikar da ita tashi Ayrah tai damuwa da ba'kin ciki ya gama rufeta da'kyar ta juya tana shiga part d'in nasu aje wayar hannunta Abidah tai tana mi'kewa tace. "Bari nabi bayanta kar tayi Mana sata kinsan 'yar 6arayi ce" Nadiya ma dake tsaye bin bayanta tai tana cewa "toni kuma nayi zaman me nima biyo ki zanyi naga aikin dana sakata zatai ne ko kuma tafi 'karfi'' shiga sukai suka tararta a cikin toilet ta d'aure hijab din'ta tana wankewa Kai Nadiya ta jinjina tana juyawa ta bud'e fridge d'in dakinsu ta d'auko karamin bokiti fal da ruwa da alama yana da matukar sanyi domin bokitin har ra6a yake kuma saboda ita suka cikashi da ruwa su saka a fridge yayi sanyi juyawa tai tana shiga toilet d'in cike da mugunta ta d'aga batare da Ayrah ta sani ba sai jin saukar sassanyan ruwa tai a jikinta 'kara ta saki cikin firgici jikinta yana kakkarwa ta d'ago tana kallon Nadiya data saka yatsanta saman lips dinta alamar tai mata tsitt batasan jin koda tari kafin tace. "Ci gaba da abinda kikeyi ko na fasa miki baki" Ayrah batace komai ba ta du'ka taci gaba da wanki yayin da Abidah ma ta d'ebo wasu ruwan a jakar faro tana zuwa tace "da wannan ruwan zaki wanke mana an fad'a miki mu matsiyata ne irinki da zamuyi wanki da ruwan fanfo ki dau'ki wannan kiyi mana shi kuma kiyi sauri kizo ki d'ora mana abinci wallahi na baki minti goma idan baki fito ba sai mun fasa miki jiki zaki gani kuma karki fito muna daidai dake" tana fad'in haka ta juya hawaye Ayrah ta goge tana jin yadda sanyi yake ratsa mata ga6o6i tana wankin hawaye na d'iga a cikin ruwan harta gama ta fita garden ta shanya musu sannan ta dawo ta d'ora musu girki data gama tana ajewa a dinning zata wuce part d'inta Abidah tai wuf tace. "Gidan ubanwa zakije dama mun sallame kine"?. Tsayawa Ayrah tai bata iya koda motsa le6enta ba saboda wani irin zazza'bi da taji yana shirin kamata dawowa tai Abidah dake binta da kallon banza a wula'kance tace "ki wuce bedroom d'in mu ki gyara mana shi tas har 'kar'kashin gado ki sharo shi sosai sannan ki had'a min ruwan wanka" numfashi me zafi Ayrah ta fitar muryarta na kakkarwa saboda sanyin AC dake 'kara taso mata da zazza'bin da'kyar tace "bani da lafiya bazan iya gyarawa ba saidai anjima" zaro ido Abidah tai tana cewa "ina ruwana da zazza'bin ki zaki wuce ki gyara mana ko saina d'auke ki da mari" tana rufe baki taji an bud'o kofa ganin wanda ya shigo ga wani irin kallon 6acin rai da yake binsu dashi yasa da gudu suka mi'ke a gigice suka shige part d'in Hajiya Khubura ajiyar zuciya Ayrah ta sauke tare da fad'in alhamdulillah daidai Aiman ya karaso ta kalleta ganin yadda take rawar d'ari yace. "Baki da lafiya ne"? Kaita d'aga muryarta na rawa tace "eh zazza'bi nake ji". "Dama baki da lafiya kuma baki fad'a min ba me ya ji'ka miki jiki haka"? Ya fad'a yana kallon yadda hijab din'ta yake ji'ke ko bata fad'a ba yasan su Abidah ne sukai mata haka "Ina tambayarki kinyu min shiru"?. "Abidah ce ta watsa min ruwa" ta fad'a hawaye yana zubo mata kaiya jinjina yana kallon kofar part din Hajiya Khubura da suka shiga yace "ok kinga kiyi shiru daina kukan zanyi wa Daddy magana idan ya dawo jeki part d'inki bari na sayo miki magani ina zuwa" juyawa yayi ya fita itama da sauri ta shige part d'inta tana zuwa ta wuce toilet ta cire kayan jikinta daya ji'ke sannan ta fito tasa wasu ta kwanta saboda jikinta ya zama kamar wuta tsabar zafin ciwon zazza'bin dake cin jikinta. Hajiya Khubura tana zaune a bedroom tana waya da d'anta Khaleel sai ganin su Abidah tai sun shigo aguje harda ihunsu a firgice ta cire wayar daga kunnenta tana kallon yadda suka hargitse tace "lafiya meya faru ihun me kuke"? Nuna kofa Nadiya keyi da hannu tana cewa "Aiman ne". "Aiman me kukai masa ya biyo ku har part d'ina dan raini"? Abidah na huci tace "dan kawai nasa wannan shegiyar yarinyar ta wanke mana hijab d'in zuwa islamiyya akan haka ya biyo mu zai dake mu". "Ya dake ku saboda bashi da hankali? Aiko wallahi dana d'ebo masa hukuma yau saiya gane ruwa ba sa'an kwando bane yanzun yana ina"? Ta tambaya tana kallon kofa gani take kamar zai shigo. "Yana parlor nasan bai fita a gidan ba jiran mu yake mu fita". "Ku fita yayi muku ubansa wannan akwai tambad'addan yaro gabadaya yabi ya hanamu zaman lafiya a gidan nan humm bari Alhaji ya dawo na rantse da Allah sai yayi mana iyaka dashi idan ba haka ba ko kad'an bazai ri'ka bari kuna iya zaman parlon ba saboda ba gidan ubanku bane shima ba gidan ubansa bane duk ranar da yayi muku gori kar kuji tsoron sa ku rama sawa tace kuyi masa tas zagi na tozarci sannan ya dakeku ya daki kud'insa muje parlon" ta fad'a tana wucewa gaba suka bi bayanta cikin d'ari-d'ari ganin baya nan yasa Nadiya jan tsaki tana cewa. "Gaskiya wannan gayen anyi mugu haba dan tsaraba ace ganinsa yasa mutum ya rud'e" ta'be baki Abidah tai tana jijjiga kai tace "hummm ina jiran fitarsa ai na shiga part nata naci uwar uwarta dan wallahi bazanyi wannan gudun a banza ba" Abidah na rufe baki Nadiya tace "to kema kenan balle kuma ni yau tsabar dukan da zanyi mata saita kasa tash................ Bata karasa ba taja bakinta tai shiru tana rarraba ido ganin Aiman ya shigo da leda a hannunsa tsayawa yayi yana kallon su fuskarsa a had'e yace "ban baku ha'kuri ba duk wacce a cikin ku take jin ta isa ita 'yar iskan kanta ce idan na fita ta ta'ba lafiyar Ayrah zan nuna muku karshen rashin kunya" yana fad'in haka ya wuce da harara Hajiya Khubura tabi bayansa ganin ya bud'e kofa ya shiga tace "mitsiyaci mara mutunci ai wallahi duk ranar daka sake dakar min 'ya'ya nima zakaga yadda ake wasan tsutsa a rana saina had'aka da hukuma" mayar da hankalinta kansu tai tana cewa "kuje kitchen ku d'ora mana wani abu da zamu ci tunda yana gidan ba bari zaiyi tayi mana aikin komai ba saidai aikin da zakuyi bashi taci domin saita biya ko daga baya" ta fad'a tana zama domin tunda suka fito a tsaye take wucewa su Abidah sukai suka fara aiki suna sake shirya plan d'in abinda zasuyi mata kawai sai ganin Aiman sukai ya shiga kitchen d'in rawa jikinsu ya farayi yana tsaye a kofar kitchen d'in ba damar da zasu fita ransa a mugun 'bace yake kallonsu yace. "Daga yau zan kashe muku warning na 'karshe akan takurawa Ayrah wallahi tallahi na rantse da Allah duk ranar da tsautsayi yasa na sake shigowa gidan nan na tarar kun sakata aiki ko kuna yi mata wani abu da bai gamshe niba humm abinda zan aikata muku bazai fad'u ba saboda munin matakin dazan d'auka a kanku domin gidan nan gidan mahaifin tane ba gidan ubanku ba baku Isa ku hanata sakewa da jin dad'i ba kaddara ce zata gitta na sake zuwa naga kunyi abu sa6anin fahimta ta zakuga abinda zai biyo baya" ya karasa maganar yana shiga kitchen d'in da sauri suka antayo waje da gudu suka baro kitchen d'in tea Aiman ya dafawa Ayrah saboda tace iya shi zata sha ya zuba a cup baisa mata komai a ciki ba ya d'auka ya koma d'akin nata tana kwance har lokacin aje kofin yayi yana kallon ta yace. "Ayrah tashi ki kar'ba kisha magani" ya fad'a yana d'an yaye rufin datai juyi tai da'kyar ta tashi zaune tana jingina bayanta a jikin fuskar gadon tea d'in ya mi'ka mata yana 6allo maganin ya bata kar'ba tai tana sakawa a bakinta tasa ruwan tea d'in ta had'iye mi'ka masa sauran tai zata koma ta kwanta yace "karki kwanta ci wannan ko guda biyu ne" kaita girgiza tana cewa "a'a bazan iya ciba saidai anjima" tana fad'in haka ta kwanta tare da lullu'ba shiru yayi yana kallon ta zuciyarsa na zafi ganin yadda suke neman kasheta da azabarsu Daddy yana sane ya'ki d'aukar mataki shi zai d'auka da kansa zaiyi maganin abun huuuuuuhh ya sauke ajiyar zuciya yana du'kawa ya rufeta kafin ya d'ago yana cewa "shikenan zan tafi idan an jima zan dawo" kaita d'aga a hankali tana cewa "nagode Yaya Aiman Allah ya saka da alkhairi" "Amin" yace yana juyawa ya fita babu kowa a parlon jinjina kai yayi yana wucewa yace "ina daidai daku zan kamaku zakuyi bayani nine maganin ku" saida suka ji fitarsa daga gidan sannan suka samu damar fitowa sukai abinda zasuyi".................................. ✍️Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë 🌺. We will meet again. Yusrah Musa Abubakar YUSEEN AL-AMEEN CE. TYPING 📲Wed Mar12/25 10:42AM YUSRAH MUSA ABUBAKAR ✨✨. 👑 ROYALTY 👑 ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫 Home of hospitality and harmony gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan ta haka taken mu yake tafiyar mu babu rago babu maci amana tsantsan gaskiya muke nunawa. STORY WRITTEN ND EDITING Yusrah Musa Abubakar Maman little Zarahn Aunty. 3~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Shahidina. @YUSRAHMS CE Page 05 & 06 Washe da yake weekend ne Baby tana bedroom har kusan qarfe goma da rabi Khairat tayi iya kokari taga ta tasheta amma ta'ki tashi da tayi magana saidai ta sake gyara kwanciya taja bargo ha'kura tai ta rabu da ita zuwa sha biyu sultan ya shigo yana cewa "Aunty Baby ki tashi" bud'e ido Baby tai tana kallon sa cikin muryar barci tace "meya faru kake tashi na"? Da serious face yace "Yaya Ahmad ne yake nemanki" zaro ido tai tana tashi zaune tace "Yaya Ahmad kuma me zanyi masa nidai nasan ko jiya bamu had'u dashi ba harna kwanta tunda yasa na buge kafata lokacin da zan canzo hijab yanzu kuma yake nemana" juyawa Sultan yayi yana cewa "Nima bansan me zaki masa ba yace dai mu taho tare karna rigaki zuwa" jin abinda yace gashi harya kusa fita daga d'akin yasa Baby mi'kewa da sauri tana cewa "Sultan ka jirani man so kake yaga kamar banji maganarsa ba"? Kai Sultan ya girgiza yana cewa "a'a cewa yayi idan na bari kika rigani zuwa gunsa tunda yau weekend ne wuni zanyi ina hawan bango da tsallen kwad'o" dirowa Baby tai tana cewa. "Kuma nifa so kake ya kashe ni kenan gara kai zai iya 'kyale ka amma ni yau me cetona saidai Abba dan Allah Sultan ka jirani" tsayawa yayi yana cewa "to kiyi sauri man gaskiya zaki jawo min aiki fa" tun bai rufe baki ba ta d'auko hijab tasa tana cewa "muje to kar lokacin daya d'iba ya fita yana ina"? Fita sukai Sultan na cewa "yana part d'insa fa" a firgice Baby tace "part d'insa kuma innalillahi na shiga uku" ta fad'a daidai sun fito parlor Mami tana zaune amma tsabar rufewa da idon Baby yayi bata lura da ita ba har suka fita suna shiga part d'in su Ahmad da prince Hamid suka fara cin karo zai fita da sauri Baby tace. "Yaya Hamid dan Allah ka taimaka min" kallonta yayi da alamar tambaya yace "meya faru"? Kaita girgiza tana kallon ko'ina kar tayi magana Ahmad yana kusa ya jita ganin baya nan tace "Yaya Ahmad ne yake nema na". "Yake nemanki me kikai masa"?. "Wallahi ban sani ba Yaya Hamid ina kwance Sultan yaje ya tashe ni wai nazo". "Ok kinga karki d'aga hankalinki ba wani abu bane tunda ba laifi kikai masa ba jeki kar lokaci ya 'kure" ya fad'a yana wucewa ya fita yana fita sukaga Ahmad ya bud'o kofa daga shi sai farar singlet da three quarter d'in wando gabanta ne ya fad'i da sauri ta karasa daidai ya zauna yace "Baby meyasa tun d'azu na tura kiranki sai yanzu kikaga damar zuwa"? Dur'kusawa tai tana cewa "Yaya ina kwana"?. "Ban kwana ba aiba wannan na tambaye kiba ki bani amsar da nake son ji meyasa baki zo akan lokaci ba raini ko"?. "A'a wallahi Yaya ban tsaya a ko'ina ba". "Ok 'karya nake kenan kinzo daidai lokacin da nace ko"? Ya tambaya yana d'agowa ya kalleta da sauri ta girgiza kai tana cewa "a'a dan Allah kayi hakuri" bai tanka mata ba sai Sultan daya kalla yana cewa "kai kuma meka tsaya kallo kana bukatar wani abu ne"? Kai Sultan ya girgiza yana cewa "a'a". "Fita a nan". Tun Ahmad ya rufe baki Sultan ya nufi kofar fita da sauri dakatar dashi Ähmäd yayi yana cewa "kai dawo min nan" cak Sultan ya tsaya a yadda ya d'aga kafarsa baiyi gaba ya ajeta ba bai dawo baya ya ajeta ba cike da tsoro ya had'iye yawu. "Bakaji abinda nace maka ba saina tashi? zomin nan" cikin azama Sultan ya dawo yana zama kusa da inda Baby take yace "kayi ha'kuri Yaya" rufe ido Ahmad yai yana cewa "6ace min da gani" da gudu ya mi'ke yana fita yabar iya Baby wacce ta gama rud'ewa bata son ta ganta daga ita sai Ahmad a guri hakan razanata yake shiru tai tana sauraron taji me zaice amma dai baiyi magana har kafafunta suka gaji sakamakon a dur'kushe take jin suna mata ciwo kuma bata so tayi motsi yace wani abu yasa ta d'aure shi kuwa tun lokacin da yace Sultan ya fita idonsa yake rufe baisan ma a wanne yanayi take ba tayi matukar gajiya amma bata da damar ce masa meyasa ya tsayar da ita haka taci gaba da ha'kuri har yai ra'ayin kansa taji yace. "Baby". Da sauri ta amsa dan tasan duk hakan wani tarkon yake son had'a mata tace. "Na'am" "Shiga ki wanke min toilet zanyi wanka". Da mamaki ta d'ago tana kallonsa ganin idonsa a rufe yasa ta samu damar iya kallonsa a ranta tana cewa "ikon Allah salon da kuma ya d'auko kenan yanzu nice zan dawo mai wanke masa toile............... Bata karasa ba taji yace "Baby mene kike kallo na ko banida matsayin dazan saka ki aiki naga kin shiga jin mamaki ko"? Mi'kewa tai tana cewa "a'a Yaya kayi hakuri bari na wanke maka" ta fad'a tana shiga "ki had'a min ruwan wanka no hot no cool" ya fad'a har lokacin bai bud'e idonsa ba shiga Baby tai tana 'karewa bedroom d'in kallo ya tsaru sosai tabd'i kamar d'akin mace irin wannan kayan 'kyale-'kyale haka abun ban sha'awa har batasan lokacin data karasa gaban wani tsuntsun roba me kama da tantabara ya baza fuka fukansa anyi masa kwalliya da blue da white d'in kala yayi kyau sosai ta kasan kafofinsa an rubuta ZUHRA da manyan ba'ki da sabon mamaki take kallon sunan amma dai ba ita Zuhran yake nufi ba watace dabam dama Yaya Ahmad yana da budurwa a hakan gashi sunan su iri d'aya da alama itama halinsu d'aya dashi dan tasan a yadda Ahmad yake bazai auri mace wacce ba irin ra'ayin sane da ita ba to amma a ina take? Ta tambayi zuciyarta shiru tai can ta tuna abinda ya kawota bedroom d'in ta manta a inda take tsabar shagala da 'kawar d'akin datai afujajan ta wuce toilet ta had'a masa ruwan bayan ta wanke ta fito kenan ya shigo had'a ido sukai da sauri tayi kasa dakai tana cewa. "Yaya na had'a maka" bai kulata ba saida ya wuce ya kusa shiga bathroom d'in sannan ya dakata batare daya juyo ba yace "ki jirani a parlor kada kije ko'ina" had'iye wani yawun tashin hankali tai da'kyar tace "to" sannan ta samu a hankali ta d'aga kafarta ta fita parlon ta samu guri ta zauna kamar yadda ya umarceta saidai tambayar dake ranta shine akan me zai tsayar da ita me kuma zatai masa to idan tajira shi ya fito me zaiyi mata kodan batai laifin dazai daketa ba shiyasa yake 'ka'kale 'ka'kale dan ya samu mafaka shigowar prince Hamid daya dawo saboda shima ya kasa nutsuwa sakamakon ganin Babyn a part d'in Ahmad kar yaci zalinta yasa ya dawo aiko yana shigowa ya ganta zaune dakatawa yayi yana cewa ''Baby zaman me kike kuma ina Ahmad d'in"?. "Yana wanka cewa yayi na jirashi kar naje ko'ina" jin abinda tace yasa ya jinjina kai bai sake magana ba ya wuce yana bud'e bedroom d'in Ahmad ya shiga bai fito ba tsayawa yayi har ya gama wankan ya fito ganinsa yasa prince Hamid had'e rai yana cewa "Ahmad meyasa ka tsayar da Baby a parlor bayan ba wata tsiyar zatai maka ba"? Kallonsa Ahmad yayi batare da ya bashi amsa ba ya wuce gaba mirror yana ri'ke da karamin towel a hannunsa yana goge jikinsa karasawa prince Hamid yai yana cewa "Ahmad na sani kana son yarinyar nan tun tasowarta amma meyasa kake koyar da ita jin tsoron ka bazaka ji dad'i ba a gaba fa saboda idan ka aurenta kafin ta saba dakai za'a dau'ki lokaci mai tsawo kai baka tunanin hakan ne"? Kai Ahmad ya jinjina yana had'e yatsun hannunsa guda biyu ya muza suka bada wani kalar sauti kafin yace. "Bana yi saboda bana son wargi maganar na koyar da ita tsorona wannan ba haka bane ina kula da rayuwarsu ne ta hanyar nuna musu bazasu sake ba idan Ina nan hakan ma tarbiyya ce ba ina takura musu saboda zalunci bane kamar yadda kai kake zatona ina kokarin ganin cewa sun zama na kirki masu ladabi wanda za'ai alfahari dasu fatan yanxu ka fahimce ni Abdul-Hamid Aliyuddeen Sharfaddeen"? Numfashi prince Hamid ya sauke yana cewa. "Ok na fahimta amma Ahmad abunne yana yawa wallahi musamman akan ita Babyn bakai mata da sau'ki gara Khairat da Sultan ma meyasa kafi matsa mata". "saboda so". Kawai shine abinda Ahmad yace yana baro gaban mirror ya dawo ya bud'e wardrobe zai dau'ki kaya prince Hamid dake binsa da kallon mamaki yace "ban gane saboda so kafi matsa mata ba? ba wannan ce amsar daya kamata kaban ba". "Wacce kake son ji"?. "So nake ka fad'a min meyasa kafi matsa mata a cikinsu kace wani saboda so niban yarda ba wanda kake so baka son ganinsa a damuwa ko kaganshi yana kuka amma kaifa kaine zaka daketa da kanka sannan kace sone wanne irin son ne wannan da mutum zai ri'ka cutarka kuma yace sone"? Ahmad yana sauraron sa amma bai bashi amsa ba saida yasa kaya ya gama abinda yake sannan ya juyo 6angaren da prince Hamid d'in yake tsaye ganin irin kallon da yake masa yasa ya saki murmushi yana cije lips yace. "Abdul-Hamid bansan yaushe ka koyi saka ido ba ada babu ruwanka amma yanzu abu ko babu kai saika d'auka meyasa kake shiga rayuwar wani kaima kaji da kanka man"? Qara had'e rai prince Hamid yayi yana cewa "ni ba wannan na tambaye kaba ka fad'a dalilin ka na takura mata shine kawai amsar da zaka ban kuma ka tabbata ka fad'a min abinda zan yarda dakai meyasa wacce kake sonta kafi matsa mata"?. "Ok kaima kana son koya ne kake so na fad'a maka"? Ahmad ya tambaya yana d'auke masa gira da sauri prince Hamid ya girgiza kai yana cewa "wa nii? Allah ya sauwake na zama mugu dai kamarka bana fata damuwa ta ka fad'a min ta yadda akai mugunta ta zama so"? Murmushi Ahmad yai yana cewa "ta yadda ake yi man saboda ina sonta yasa nake takura mata nake bata horo a koda yashe domin nine zan zauna da abata sannan son da nake mata bana yi mata ko kaina bana yiwa na damu da ita fiye da yadda kake tunani bana jin dad'i idan har ban ganta ba domin itace mahad'in rayuwata mother of my kids bani da kamarta fatan yanzun ka gane abinda nake nufi"?. Wani kallon uku saura kwata prince Hamid yayi masa a she'ke yace "au haba a hakan ta zama duk wadannan abubuwan daka lissafo"? Kaiya jinjina yana cewa "kwarai kuwa ko kana tantama ne"?. "Eh taya kake tunanin zan yarda dakai da abinda ka fad'a"?. "Ta yadda ake yarda man". "Toni bazan yarda dakai ba Ahmad domin ba gaskiya bane abinda ka fad'a kawai dai kayi hakan ne dan ka kare kanka kuma baka isa ba". "Ok zaka hana kenan a bani ita tunda kaine ka haifeta ko"?. "Ban haifeta ba amma idan nacewa Abba ya hanaka aurenta ko kuma naje gurin Sultan Sharfaddeen nakai 'kararka akan abinda kake mata shikenan na kashe case d'in taka tazo karshe zaka gane kurenka kaima ka koma hannun 'yan sari". "Da gaske? Humm idan kai haka zaka matukar burgeni saidai ka sani ko ramin gyare zaka kai qara ta bazan fasa auren Baby ba idan kuma kaga ban aureta ba to d'ayan biyu kodai ita koni wani ya mutu ko kuma dama can ita ba matata bace domin wannan yarinyar da kake gani rayuwata ce ita bani da kamarta kaima kasani saidai ka'ki fad'ar gaskiya sonta a raina yake duk wani motsi da zanyi da sonta nake motsawa I hope yanzun ka yarda"? Kai prince Hamid ya girgiza yana cewa. "Da sau'ki dai". "Ok baka yarda ba kenan"?. "Eh kusa da gun idan kana so na yarda dakai da abinda ka fad'a to daga yau karka qara dukan Baby ko kuma ka daina mata tsawa sannan ka dawo lalla6ata ta yadda zata saki jiki dakai har itama ta daina tsoronka ta kamu da sonka domin yanxu itakam a cikin zucuyarta tsoron kane fal ya cikata da ace tasan kana sonta to wallahi da tsoronka da zataji sai yafi haka maybe kasa zuciyarta ta buga ko ta kamu da ciwon firgita shiyasa nake sake fad'a maka abinda xai fisheka please Ahmad dan Allah ka daina baiwa yarinyar nan barazana idan kuwa ka'ki jin maganata hummm abun zaizo maka a baibai kai ko koyi bakai da Shadad kana gani yadda yake kula da Khairat saboda yana sonta koda ace ita da Baby sukai laifi saidai ya hukunta iya Babyn ita ya rabu da ita ko kuma ya hukunta su tare sannan ita Khairat d'in yazo yana lallashinta daga baya amma kai babu ruwanka wanda kake so shi yafi shan wahalarka meyasa hakan"?. "Ni haka nawa tsarin yake aini dashi ba d'aya muke ba kowa daban shi Shadad sunansa ni kuma Ahmad sannan halin mu ba d'aya bane kowa da nasa bazan iya daina hukunta Baby idan tayi laifi a gidan nan ba saidai idan bana nan ba ina haka dan na zalunceta ko nasaka mata tsoro na a zuciyarta bane a'a ko d'aya ina so na horar da abata da kaina domin koma mene nine xan zauna da kayata tsahon lokaci tunda aurenta zanyi ya kamata kaima ka fahimce ni". Kai prince Hamid ya jinjina yana cewa "ok shikenan Ahmad na fahimce ka amma dai dan Allah ka ri'ka rage wasu abubuwan" yana fad'in haka ya juya ya fita Ahmad kam bai fita ba saida ya gama abinda yake yi sannan ya d'auko wani abu kamar gift🎁 ya fito dashi har lokacin Baby tana nan zaune mi'ka mata yai yana cewa "kiyi amfani dashi kuma ban baki dan kiyi kwalliya dashi ba duk ranar da naga abun nan a jikin ki ko kin ajeshi hummm tashi ki tafi" kar'ba tai tayi masa godiya ta fita da mamaki a ranta har tayi hanyar part d'insu ta fasa ta shiga part d'in Momy suna zaune ita da Khairat ta shiga da sallama tana zama ta gaida Momy amsawa Momy tai tana kallon ta da murmushi kamar batasan daga inda take ba dan prince Hamid ya fad'a mata amma sai tace "Baby daga ina wannan kuma fa"? Sauke numfashi Baby tai tana waiwayen kofar shigowa ganin ba kowa tace "ya Ahmad ne ya bani yanzu". "Ya Ahmad kuma"? Khairat ta tambaya tana zaro ido tace "tofa abun ya motsa mene a ciki bud'e mu gani" huuuuuuhh Baby tayi ajiyar zuciya tana cewa "yace bai bani dan naje na ajiye ba sannan idan nayi kwalliya dashi nasan sauran kuma idan na'ki amfani dashi hummm kawai yace min kinsan abun bazaiyi kyau ba". "Ban gane karki yi amfani dashi ba sannan idan kika ajiye kinsan sauran ji Yaya Ahmad da saka mutum a tsaka me wuya" Khairat na rufe baki Baby tace "dan Allah Aunty Khairat kiyi shiru karya shigo ya jiki indai dan wannan abun ne bari na bud'e mu gani" ta fad'a tana cire d'an golden d'in 'kyallen da aka d'aure ta aje a gefe tana bud'ewa duk zaro ido waje sukai ganin wani d'an kyakkyawan littafi ne a ciki kallon juna sukai Khairat data d'auko littafin tana kallo tace. "Kai amma fa gaskiya yayi kyau to amma taya zaki kwalliya da littafi da yake cewa kar kiyi ado dashi"?. "Oho wallahi nima bansan manufarsa ba" Baby ta fad'a itama tana qarewa littafin kallo murmushi Momy tai tana cewa "da yace karkiyi kwalliya dashi yana nufin karki ajeshi akan mirror ko drawer ya zama bakya karantawa kin gane"? Kai Baby ta jinjina zatai magana Ahmad ya shiga da sauri ta kar'be littafin daga hannun Khairat wacce itama ta cillo mata duk da ya gani kawai ya sharesu ne maidawa ciki tai tana mi'kewa zatai waje Khairat ma ta mi'ke tana cewa "Baby jirani mu tafi" tun kafin Baby tace to Ahmad yace "ku dawo min nan wato saboda ga macuci ya shigo ko"? Duk tsayawa sukai baby kam da yake ta kusa kofar fita da sauri ta dawo Khairat kuwa dama iya mi'kewa tai dole suka zauna kowacce tana ankare sun kama kansu gudun yin laifi iya shida Momy suke magana har wani lokaci sannan ya kallesu ganin yadda suke a takure yace. "Me kuke jira baku tafi ba ko gulmar zancen da muke kuke yi"? Ba suba da yaiwa tambayar hatta Momy saida ta kalleshi da mamaki tana cewa "amma kaine fa kace su dawo har zasu fita ka tsayar dasu". "No Momy da nace su dawo ai ba'a nan nake nufin su zauna ba" ya karasa maganar yana mayar da hankalinsa kansu yace "kai daku fa nake ku barmin nan" aguje suka mi'ke har suna gware wajen fita suna ficewa a part d'in Khairat ta sauke ajiyar zuciya tana huci tace "innalillahi kai jama'a indai Yaya Ahmad yana gida bazai ta'ba bari kai 'kiba ba wai zamu fito yace mu tsaya sannan mun tsaya yace me muke jira ko gulman zancen da suke muke yi" kai Baby ta girgiza jin ana kiran sallah tace "nikam bani da bakin magana Aunty Khairat yau babu abinda naci ko breakfast banyi ba". "Ked'in me kike har yanzu baki karya ba"?. "Ina barci fa Sultan ya kirani wai nazo inji ya Ahmad wallahi bakiji yadda naji zuciyata tana bugawa ba saida nazo naji ba laifi nayi masa ba toilet zan wanke masa na had'a masa ruwan wanka". "Ina masu yi masa hidima da saiya kiraki"?. "Oho musu ni banga kowa ba dana shiga" kai Khairat ta jinjina tana cewa "nikam dama na dad'e ban shiga part d'insu ba yanzu kece a online kafin abun ya juyo kaina" ta fad'a daidai sun shiga part d'in Mami tana zaune Sultan yana kusa da ita yana aikin daya saba na shagwa'ba farko da yaji an bud'o kofa ya d'auka Ahmad ne harya nutsu ganin su Baby yasa yaci gaba dariya Khairat tai tana cewa "lallai yaron nan Sultan kana lokaci amma fa kayi a hankali dan ya Ahmad yana nan zuwa idan ya kamaka kana wannan shagwa'bar yau zakai bayani" kamar ba dashi take ba haka yaci gaba da abinda yake yi kuma abinci ake bashi a baki amma yana had'iyewa zaici gaba kai Baby ta jinjina tana cewa. "Hummm rabu dashi Aunty Khairat maybe kaddara ce take jansa idan yana da rabon shan duka ne yaci gaba ya Ähmäd roba ne yana daidai da 'kugun kowa kaci gaba dayin shagwa'barka lokacin kane dama ka samu tunda kai ba'a fiya takura maka kamar niba" ta karasa maganar tana wucewa bedroom ta aje littafin ta shiga toilet tayi brush ta fito tana dawowa parlor ta wuce dinning zamanta keda wuya taji sallamar Ahmad ya shigo ji tayi abincin ya 'kwareta da sauri ta dau'ki ruwa tasha Khairat na can gefe nesa dasu Mami Sultan kuwa tuni ya daidai kansa ya nutsu sosai a hankali yasa hannu yana kokarin kar'bar spoon d'in dake ri'ke a hannun Mami dan kada Ahmad ya gani kallonsa Mami tai tana cewa. "Ya haka Sultan ka bari na karasa baka man"? Kaiya girgiza yana kallon Ahmad yace "a'a Mami zan qarasa da kaina" ya fad'a yana kar'ba da sauri ya mi'ke bai karasa ci a gurin ba ya koma can saman dinning ya zauna kamar gaske ya ri'ka she'ka loma da ana bashi yana shagwa'ba kamar baby zatai dariya haka ta zuba masa ido tana kallon sa zuwa wani lokaci ta kallo parlor ganin hankalin Ahmad baya kansu zance kawai suke da Mami yasa tai qasa da murya tana cewa. "A'a autan Mami yau kuma yada cin abinci da kanka wato ganin boss Ahmad yasa ka nutsu ko? Wallahi naso lokacin da muka shigo sannan shima ya shigo ya sameka kana shagwa'ba humm ya fasa bakin shagwa'bar sannan yau ka wuni har dare kana kar'bar service" d'agowa Sultan yayi yana kallon ta kamar bazai magana ba ya mayar da hankalinsa kan cin abincin saida ya gama ya dau'ki tissue ya goge bakinsa ya aje sannan yace "ai bazan yarda nayi abinda zai dakeni ba domin niba jaki bane kalli man Ina da hanyar kare kaina yana shiga na nutsu na tattara ya nawa yanawa na baro gurinsa hanyar lafiya a bita da shekara ban zauna bama balle yace nayi kuskuren wani abu kuma da salona kuka d'auka daga yau bazai sake kamaku da laifin wani abu ba balle ya hukunta ku" murmushi Baby tai tana girgiza kai tace "humm Sultan da alama ka manta waye ya Ahmad duk abinda muke yana hankalce damu wallahi ra'ayin kula kane baiyi ba da yaso zakaji yayi magana tun lokacin daya shigo ai ya ganka ana baka abinci a baki kuma yaga shagwa'bar da kake yi mata amma da baiyi niyyar yace maka komai ba kana gani ko inda kake bai kalla ba kawai kai dai kace kana da sa'a mukam bamu da bakin magana saidai muce alhamdulillah" qara qasa da murya Sultan yayi yana cewa "Aunty Baby na fad'a miki mafita ta yadda bazaki sake shiga tarkon Yaya Ahmad ba"? Kaita girgiza tana kallon sa tace. "kaima ba tsira kayi daga tarkon nasa ba kayita kanka kafin kayita wani". "Allah Aunty Baby da gaske nake". "Da gaske kake me"?. "Shawara zan baki akan hakan". "A'a bana bu'katar shawara saidai basir indai akan ya Ahmad ne duk ta inda ka 6ullo zaka sameshi yana kofar shima a tsaye yana jiranka da akwai inda zai 6ullo maka dan haka kaima kaji da kanka baka da wata shawara da zaka bayar anan". "Amma Aunty baby ai baki bari kinji me zance miki ba"?. "Nifa basai kace komai ba Sultan na fahimta ka 'kyale ni dan Allah karka d'aga min hankali na kasa cin abinci kai ka gama ci" mi'kewa yayi yana cewa "shikenan tunda bakya son ji na fad'awa Aunty Khairat" Baby na kokarin 'kara zuba abinci a place tace "yauwa saidai itan zaku daidaita amma dai banda ni kome zanyi ya Ahmad bazai fasa d'irka taba" ta karasa maganar tana d'agowa ta kallo inda yake magana suke sosai da Mami cikin sakewa kaita jinjina tana fara cin abincinta tana kallon Sultan yadda ya zauna a kusa da Khairat ya kifa kansa qasa yana fad'a mata abubuwa ita kuma tana d'aga kai tana murmushi wani lokaci kuma tad'an zaro ido ta rufe baki cije lips Baby tai a ranta tace ''tabd'ijan da ace ya Ahmad zai ganku a haka humm yanzu jikinku zaiyi d'umi" ta'be baki tai tana mayar da hankalinta kan cin abincinta har Ahmad suka gama zance da Mami ya tashi yayi waje yana fita Sultan ya dau'ki mp zai kunna Mami tace. "Wallahi Sultan ka kiyayi kanka ka guji had'uwarka da Ahmad akan wannan mp idan ba duka kake nema ba maybe yanzu ka ganshi ya dawo saboda akwai shi da wasan baya domin irinku marasa jin magana balle yaga duk ku ukun kuna part d'in". Zama Sultan yayi yana kokarin kunnawa yace "ai Mami nasan bazai dawo ba ya fita kenan". "Au haka kace saboda ya fad'a maka dazai fita cewa bazai dawo ba"? To ai shikenan nidai kasan ba tankawa zanyi ba idan ma ya kamaka kaine jikin ka zaiyi tsami". "Ai Mami inada kafar gudu bazan zauna ya riske niba ni ba irin Aunty Baby bane dazan tsaya ina gani ya ri'ke ni ko zomo bazai fad'a min zilliya ba yasin saidai muyita zaga masarautar nan da gudu har ya gaji ya barni". Kai Mami ta jinjina tana sakin murmushin zancen nasa tace "lallai kam amma shikenan ba matsala bansan shirinka ba nidai na fad'a maka kar tsautsayi ne yake janka a kowanne lokaci zaka iya ganinsa ya dawo kuma ba ruwana nidai na fad'a maka gara kaji dakyau kar kace baka sani ba ko kayi tunanin zan bashi hakuri ya 'kyale ka ina kallo zaiyi maka shegen duka" tana rufe baki Sultan ya d'ago zaiyi magana sai ganin Ahmad yai ya bud'o kofa kamar a mafarki yana cewa "Mami nabar key d'in motana anan"?. Humm tabd'ijan aguje Sultan ya tashi kamar iska na cirashi sama tsabar sauri wuff ya fad'a bedroom Ahmad da baidan me yakewa gudun ba yace "shi kuma wannan fa"? Murmushi Mami tai ganin tun ba'a je ko'ina ba gashi ana shirin kama shi tace "humm Sultan nefa ai ya zama saidai addu'a" kawai haka tace saboda taga alamar kamar Ahmad d'in baiga mp dake aje a gurin ba. "Baby kira min Sultan" Ahmad ya fad'a yana qarasa shigowa parlon to Baby tace tana mi'kewa da sauri ta shiga part d'in Mami amma babu alamar Sultan kira ta fara kwalla masa ya'ki amsawa saida tace ya Ahmad ne yace yaje aiko sai gashi ya fito daga toilet yana cewa ''yana Ina"? Juyawa baby tai tana cewa "yana parlor man nidai na fad'a maka idan kaga dama kazo ko ka'ki zuwa ba ruwana tsakanin kune Kai dashi" jin abinda tace gashi tana shirin fita yasa da sauri yabi bayanta Ahmad yana tsaye a gurin da yake Sultan ya fito yana ra6ewa duk xatonsa ko Ahmad yaga mp a zahiri kuwa babu abinda ya gani kawai dai yaga ya tashi da gudu ne tambayar da zaiyi masa kenan, karasowa yayi yana cewa. "Gani Yaya kayi hakuri dan Allah" a tsume Ahmad yace "gudun me kake wato saboda kaga ban dad'e da fita ba na dawo kamar wanda kaga dodo shine harda d'ame kafa kana cin uban gudu ko"? Da sauri Sultan ya girgiza kai yana cewa "dan Allah kayi ha'kuri Yaya ba ganinka ne yasa na gudu ba gudawa nake" Sultan na rufe baki Mami ta fara dariya tana kallon yadda yake d'an ri'ke ciki kamar gudawar gaske yake tace. "Tofa Sultan wannan 'karyar har Ina kai d'in ne kake gudawa ban sani ba amma yanzu dawowar Ahmad ta kamaka ko"? Da sauri ya girgiza kai yana cewa "A'a Mami dama tun jiya da dare na fara wannan abun da kika ban naci ne". "Au 'karya zaka koya wanne abun na baka jiya wanda ya saka gudawa daga safe zuwa dare"?. "Wannan abun fa" Sultan ya fad'a yana sake ri'ke ciki yace "kinji yanzu ma cikina yana 'kugi ga ciwo wayyo Allah na" ya karasa maganar yana dur'kusawa ya fara murd'e-murd'e kamar gaske. "Uhmm" kawai shine abinda Mami tace dan tasan ya fad'a ne kawai neman hanyar tsira yake domin idan ya bari Ahmad ya fahimci dan shi ya gudu tofa saiya sakashi gudawar dole anan gun ko Kuma yace suje toilet d'in ya gani idan gaskiya ne ko kallonsa Ahmad bai sake yiba daya dau'ki key d'in zai fita yace "kaje gurin Abdul-Hamid ka kar'bi magani" da sauri Sultan yace "to". "Ba fad'in to ba idan na dawo yace bakaje ka kar'ba ba wallahi ni dakai ne a gidan nan sai naci ubanka tunda kuna son sake da lafiyarku musamman Baby" yana fad'in haka ya fice 'kak'karfar ajiyar zuciya Sultan ya sauke yana kallon Mami wacce itama ta zuba masa ido da murmushi akan fuskarta zatai magana Sultan yace "ya zanyi Mami" kaita girgiza tana cewa "a'a bansan yadda zakai ba ni babu ruwana sai kaje ka kar'bo kafin yaje inda zaije kasan ya dawo ko baka so saiya saka a gaba kasha alhali ba jinyar kake ba gara ka wuce ka kar'bo sai kazo ka ajiye". "To Mami bari na kar'bo" ya fad'a yana fita ganin Sultan ya fita Baby data mi'ke daga dinning bayan ta karasa cin abincin data zuba parlor ta dawo kusa da Mami tana zama tace "hummm yau dai bari mu d'ana zaman parlon kafin ya Ähmäd yayi yabar mana gu gaskiya wallahi Yaya Ahmad yana da matsala ba dama yabar mutum ya sha'ki iska mai kyau haba jama'a nifa na matsu naga ya koma yaushe nezai ya tafi Mami"? Kai Mami ta girgiza tana cewa "taya zan sani saidai na tambayar miki shi" zaro ido Baby tai tana kallon Sultan daya dawo ri'ke da magani dariya ta saki ba shiri tana kallon sa tace "masu gudawa sai azo asha magani ko ta sauka tunda wanda yasa ka kamu d'in ya tafi" zama Sultan yai yana sauke numfashi yace "barni Aunty Baby ai banyi tunanin zan tsira ba na d'auka zai gane 'karya nake". "Humm ai ramin 'karyar 'kurarre ne maybe daya dawo nan zai fara shigowa ya duba jikinka saidai ka ri'ka kula da kaji dawowarsa ka shige bedroom ka kwanta". "Ai Kuma idan na kwanta zan jawa kaina allura". Kallonsa Mami tai tana cewa "eh ai kaima ita kake nema tunda kai "karyar jinya kayi fatan idan ya dawo kar yasa a d'aura maka ruwa ma" Mami na rufe baki Baby da Khairat suka fara dariya ganin yadda Sultan yayi da fuska Khairat tace "humm yau wani ya fad'a tarko Allah ya fitarka lafiya boss yana nan dawowa gare ka" tashi Sultan yayi yana nufar hanyar bedroom ganin zasu d'aga masa hankali yace "wannan maganganun naku ma kad'ai she'ke ni zasuyi idan naci gaba da zama anan gara na baku gu" ya fad'a yana wucewa cikin tsokana Khairat dake kallon Mami tace. "Please Mami ki tambayawa Baby Yaya Ahmad yaushe zai tafi" Khairat na rufe baki Baby ta dafe 'kirji tana zaro ido waje tace "na shiga uku Aunty Khairat karki yala min masifa so kike yau yayi farfesu na kenan"? Dariya Khairat tai tana cewa "a'a ko d'aya ba son sani kike ba shiyasa na tuna mata ta tambaya miki ko"?. "A'a wallahi ni bance ba kawai abar maganar tashi ma muje 6angaren Sultana Addah mu ganota" ta fad'a tana mi'kewa tace "please Aunty Khairat taso mu tafi Mami dan Allah karki fad'awa Yaya Ahmad komai" kai Mami ta d'aga mata daidai Khairat ta mi'ke suka fita. ✍️Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë. Banda kamarka ya rasulullah a duniya Banda kamar ka ya rasulullah lahira. Ga Mai kyauta da aljannah irin rabon kud'i Ga Mai kure Mai bu'kata yayan imam Ali Ga Mai bayar da kyautar rai zo a hankali Zaka fahimci ba kama Tai duniya da lahira. Gashi da kyan siffa da haiba najidul awatiki in kaga sayyidil wara bakai ba ba'kin ciki ya najamul hudah Annabi dauke shamaki lamunce mu ganka ya mai salsabil da khausara. TYPING 📲+234 81 60 9 8 3 0 83 Chat with me Yusrah Musa Abubakar. 👑 ROYALTY 👑 Dedicated to my daughter Fatima Zarah Elham little Zarahn Aunty. ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫 Home of hospitality and harmony gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan ta. STORY YUSRAH CE WRITTEN YUSRAH CE EDITING YUSRAH CE Idan mutane suna nuna naka kula kaima ka nuna musu.. MRS ÄL'ÄMËËÑ ÄHMÄD ÇË 🌹. 4~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Khaifinah. @YUSRAHMS CE Page 07 & 08 Ayrah tana kwance a bedroom d'inta Abidah ta shigo da ruwa a Kofi a hannunta yaye bargon data lullu'be jikinta tai tana watsa mata ruwan tace "tashi 'yar matsiyata tun d'azu muna jiran kizo ki had'a mana breakfast ashe ke barci ma kike wato gaki isasshiya 'yar gidan isiyaku ko"? Ayrah data tashi a firgice tana sharce ruwan data watsa mata a fuskarta ga sanyi muryarta na rawa tace. "Kiyi hakuri bansan gari ya waye ba wallahi tunda nayi sallah na koma barci" wani irin ba'kin kallo Abidah tai mata tana cewa "oh baki san gari ya waye ba? To ai yanzu kin sani zaki tashi kije ki had'a mana ko saina d'auke ki da mari"? A zabure Ayrah ta mi'ke tana saukowa daga kan gadon ganin Abidan ta d'aga hannu tace "dan Allah kiyi hakuri" a tsawace Abidah tace "zaki wuce ko saina fasa miki baki" ta karasa maganar tana hankad'ota gaba suka yo waje suna fitowa parlor Hajiya Khubura dake zaune ganinsu yasa ta sakarwa Ayrah harara daidai sun karaso Ayrah ta dur'kusa tana cewa. "Ina kwana"?. "Ubanki keda kwanan 'yar gwana na nemi gaisuwarki ne ko shisshigin da kika saba zaki min hamsha'kiya daga barci kika tasheta Abidah ko kuma a zaune kawai take raini ne ya hana tazo tayi mana breakfast d'in"?. "A'a a kwance na sameta sai gwarci da munshari take kamar rago Wai Kuma na tasheta harda wani batasan gari ya waye ba". "Au batasan gari ya waye ba meyasa data fad'i haka baki buge mata baki ba ko ki sharara mata mari yadda zata wartsake da wuri ta dawo cikin hayyacinta"?. "Humm kinsan ma wani rainin hankali Umma tana tashi sai cewa tai wai wani uwarta barci ta koma bayan datai sallah kamar batasan da aiki a gabanta ba". Jawota Hajiya Khubura tai tana tula mata duka a baya tace "Iya barci kika koma ba mutuwa kikai ba naso duniyar kika bari zaki wuce ki had'a mana ko saina tashi a kanki kika zuro min wadannan mayun idanuwan naki masu kala dana mujiya" cikin takaici da 'kunan rai Ayrah ta mi'ke da'kyar take d'aga kafarta tsabar rashin dad'in da take ji a jikinta ta wuce kitchen harta bud'e kofa zata shiga ta tuna bata tambaye su me za'a dafa musu ba dawowa tai tana tsayawa daga nesa dasu ganin yadda duk suke binta da wani irin kallon rashin mutunci tasan ta karaso gurin su sai taci shegen duka muryarta a hankali tattare da damuwa tace. "Me zan had'a muku"?. A masife Nadiya ta mi'ke tana cewa "uwarki da ubanki zaki had'a mana 'yar bagidajiya kullum sai ana fad'a miki yadda zaki aiki idan kinga dama ki kawo mana d'anyan abinci ko kuma ga hanya nan ki wuce ki koma kiyi barcinki ina daidai dake a gidan nan badai gadararki Aiman ba? To wallahi koshi bai isa yai min na 'kyale shiba balle ke banza a banza da'ki'kiya ma irinki" shiru Ayrah tai kamar zata fashe da kukan ba'kin ciki ganin yadda suka saka ta a tsaka me wuya zata iya dafa abinda basa so shiyasa ta tambaye su domin mafi yawancin lokuta suna yi mata haka saita dafa musu suce bashi suke soba suyita bata wahala tana kai komo daga kitchen zuwa dinning karshe idan batai sa'a ba bayan zagi harda duka suke had'a mata.................. Aje wayar hannunta Nadiya tai tana mi'kewa tayo wajenta ganin ta tsaya bata juya ta tafi ba cikin tsawa tace "kee ubanki kike kallo? Zaki wuce kiyi abinda aka saka ki ko saina kashe ki a gun nan" ta karasa maganar tana yowa kanta da gudu Ayrah ta koma kitchen tsaki Hajiya Khubura tai tana cewa "ni wallahi na kasa gane wannan yarinya sam ace kwa'kwalwarta bata ja kullum dan masifa sai ana maimaita mata magana kamar batasan me zatai ba". "Ai Umma idan baki gane ba nasan manufarta so take tayita ja mana lokaci har wannan mara mutuncin Yayan nata Aiman ya shigo ya samu tana yi mana aiki shine dalili saboda tasan kema ba darajaki yake ba balle mu daya tsane mu kamar gidan ubansa ne bayan shima d'an karo ne gara mu munada uwa a gidan zamu taka bazarmu muyi tun'kaho shifa gidan 'kanin ubansa ne kawai bayan haka baida wani hurumi a gidan sai nuna gadara"? Abidah ta fad'a tana hararar kofar da Ayran tabi. Tsaki Hajiya Khubura tai tana cewa "gadararsa ta banza dad'in abun ma tunda ba gado ne dashi ba tanan nake godewa Allah da ace wannan mara kunyar yaron d'an gidan Alhaji ne toda na kad'e wallahi ni kaina bazai barni na huta ba zama saiya gagare ni a gidan nan balle ku saidai ku koma gidanmu to inda Allah ya rufa asiri shima a raka6e yake yana cin arziki shine dad'in abun". "Humm ya kwantar da hankalinsa zai gane kurensa a gaba sharrin da zamu shirya masa saiya gwammaci dama ya mutu kafin zuwan wannan ranar ni nasan abinda zan shirya masa kawai kuyi shiru ba tun yauba na fahimci so yake yasa sai munbar gidan nan 'karfi da yaji d'an Daddy ya share shine shiyasa yanxu ita kuma take sake hura tata wutar da zatai mana sharri kinga idan ya shigo ya tarar tana aiki ai zaiyi magana hakan yasa ta'ki wucewa tai abinda muka sakata jiran shigowar sa take ni kuma saina gwada masa aikin sharri domin sai nayi sanadin barinsa gidan nan". Duk wannan zancen da suke Nadiya tana tsaye tun lokacin data mi'ke zata bi Ayrah bata zauna ba sai yanzu ta koma ta zauna tana cewa "ai kuma tayi a banza wallahi indai ina gidan nan sai tayi aiki ba Aiman ba ko ubansa ne yazo bai isa ya hana ba idan kika ga na daina sata wahala a gidan nan d'ayan biyu ne ya faru kodai nayi aure ko kuma Umma aurenta ya mutu" tana rufe baki Hajiya Khubura ta zaro ido waje tana cewa "ke baki da hankali kike min fata aure na ya mutu kuma? Dan ubanki daina fad'a karki fad'a a bakin mala'iku yana dawowa kisa ya sakeni mu fito rana" dariya Abidah tai tana cewa "ai Nadiya muda gidan nan mutu ka raba takalmin kaza wallahi bamai fitar damu haka Umma babu inda zataje tana nan sai tayi masa takaba wa zai bar irin wannan dukiyar kina gani fa daga iya wannan yarinyar baida wani d'an to me kike zato idan akace ya mutu dukiya ta zama tamu domin wallahi ko sisi baza mu bata ba sannan saita bar gidan kota shiga duniya ko tasan inda dare yayi mata". Kai Hajiya Khubura ta jinjina tana cewa "yauwa 'yar albarka har kinsa naji dad'i domin hakan da kika fad'a har kinsa na shiga wani yanayi kawai haskoni nake dukiyar nan ta zama tawa humm akwai wada'ka dan saina mayar mana da rayuwar mu irin ta turawa yau muna wancan 'kasar gobe muna wancan 'kasar mu zaga duniya mu bud'a idanu ba zama kuma babu wanda ya isa ya tuhume mu duk wanda yayi yunkurin tarata da maganar gadon Ayrah wannan dama sunansa gawa". "Tabbas Umma kin fad'i gaskiya domin babu wanda zai taka mana burki duk wanda yayi yunkurin hakan kuwa zai had'u da bala'in da yafi karfin sa sai mun mayar da rayuwarsa abar tausayi''. Humm Allah sarki duk abinda suke Ayrah tana jinsu saboda ta d'auko plask d'in shayi data dafa zata kawo musu taji abinda suke fad'a jikinta na rawa ta juya zuwa kitchen tana kuka a ranta tana tunanin ya zatai wa zata tara da wannan maganar duk da watsar da ita da mahaifinta yayi a hakan tana son abinta batasan wani abu ya sameshi taji su suna wadannan maganganun innalillahi wa inna ilaihi raji'un Allah ya fidda mahaifin ta daga wannan tarkon da suke shirya masa Allah ya toni asirin su fasa fita takai musu tea d'in tayi kawai ta juya zuwa kitchen d'in tana kuka tsabar yadda jikinta ke rawa da abinda taji suna fad'a da'kyar ta iya karasa had'a musu abubuwan breakfast d'in sannan ta d'auko ta kawo musu fuska ba walwala tai musu serving zata tafi Abidah ta dakatar da ita ta hanyar fisgota baya tana cewa. "Ke tsaya min anan gidan ubanki zaki tafi dama mun sallame kine"? Ran Ayrah a 6ace ta d'ago tana kallon Abidah wacce ta koma tana huci ta zauna babu wanda ya kalli inda take suna ta zancen su har suka gama suka mi'ke duk sunyi banza da ita kamar sun manta da tsaiwarta a gurin parlor suka koma Hajiya Khubura dake waya bayan ta sauke ta kalli Ayrah dake tsaye kamar an dasata tana cewa. "Ita kuma wannan tsaiwar uban me take ne acan nifa bana son ganinta a parlon nan domin ba irin gurin zamanta bane ke Abidah me zatai miki kika tsayar da ita" d'agowa Abidah tai a wula'kance tace "oh nina manta da ita ma dama takalmi zata goge min zan fita anguwa" ta karasa maganar tana kallon Ayrah tace "ke zo nan ki goge min kafin na tashi tunda naga yau da wani sabon raini kika tashi kuma zanyi maganinki" ko tari Ayrah batai ba balle ta nuna taji haushin maganar da Abidan ta fad'a ba sai qarasowar datai tana shirin dur'kusawa a tsawace Abidah tace. "Da ubanki zaki goge min baki d'auko towel ba" ta fad'a tana kai mata duka da sauri Ayrah ta matsa baya dukan bai sameta ba daidai Aiman ya shigo baiga dukan da Abidah ta kai mata ba amma yaga sanda Ayran ta matsa baya fuska ba rahma ya karaso yana kallon Ayrah data sau'ke sansanyan numfashi cikin jin dad'in ganinsa har tana d'an sakin fuskata dan karya fahimci wani abu muryarta a daidai tace. "Yaya ina kwana"?. Bai amsa ba sai tambaya daya jefo mata "me kike yi anan"? D'an sauke kai tai tana cewa "babu komai". "Babu komai kike tsaye a gabansu matsawar ne naga kinyi"?. Nan ma kaita girgiza tana cewa "babu komai" ganin bazata bashi amsa ba kuma yasan wani abu suke mata amma ya share yana jinjina kai yace "ok muje" wucewa gaba tai yana bin bayanta suka shiga part d'inta da harara duk su ukun suka rakashi Hajiya Khubura data ja tsaki tace "anya wannan yaron kalau kuwa kullum yazo ya 'kule a bedroom d'inta yayi shiru kamar ya mutu ba iskanci suke yiba karfa nan da 'yan kwanaki muga ciki a jikinta dan ban yarda da wannan yawan shige da ficen nasa ba tabbas akwai wani abu a 'kasa". Ta'be baki Nadiya tai tana mi'kewa zata bar gurin tace "aiko Umma da gani babu tambaya kina ganin yadda yake mata abubuwa bayan ba uwa d'aya uba d'aya suke ba kinsan bazaiyi mata a banza ba wallahi akwai morar da yake mata kuma abinda kika fad'a saiya zama gaskiya nikan nayi anguwa" tana fad'in haka ta dau'ki handbag d'inta tai waje kai Hajiya Khubura ta jinjina tana cewa "to haka ne kenan na canka daidai iskanci yake yi da ita tabd'i aiko wallahi ba'a gidan nan ba bari Alhaji ya dawo xan fad'a masa ya dakatar da Aiman ya daina shiga d'akin ta idan yaki wata rana yana gaf daya bud'e ido yaga 'yarsa da cikin shege a cikin gidansa" dariya Abidah tai tana girgiza kai tace "a'a Umma ki kyale shi kawai karki fad'a masa dan Allah ki bari ta haihu idan cikin ya tabbata muci ragon suna musha minti". ''A gidan ubanwa zaku sha mintin kuci ragon? hummm nifa bawai cikin shegen da zatai ne damuwata ba a'a tsorona kar ace 'yar gidan mijina ce labari ya karad'e ko'ina samari su'ki zuwa neman auren ku gara idan ma cikin zaiyi mata ya bari na aurar daku ko kuma ku fara samun wanda zasu aure ku bayan an gama komai saitai cikin nasan dai duk tsiya ita da mahaifinta ne zasu shiga cikin tozarci bani ba ke wannan maganar ma tasa dole naje gurin Hajiya Basirah naji yaya meke tafiya" tana rufe baki Abidah tace "indai haka ne Umma muje na rakaki ayi komai a gabana domin duk burin da kika d'auko zan taya ki cika shi" mi'kewa Hajiya Khubura tai tana cewa. "Yauwa Abidah haka nake son ji ina so naga d'an dana haifa yana bin hanyar da nake bi bari na d'auko mayafi na mu tafi" ta fad'a tana mi'kewa ta shiga part d'inta itama Abidah mi'kewa tai tana shiga nasu part d'in ta shiryo kusan tare suka fito d'an mayafin da Hajiya Khubura tasa ko 'yar shekara sha biyar iyakaci kenan d'an karami iya kafad'arta suka fita. Aiman kam suna parlon part d'in da Ayrah take yana lallahinta da bata hakuri cewa ta daina saka damuwa a ranta komai me wucewa ne insha Allahu wata rana gaskiya zatai halinta ta daina ganin kamar Daddy baya sonta ba laifinsa bane akwai abinda basu sani ba a duhu domin bayan rasuwar mahaifiyar ta ba haka Daddyn yake mata ba kullum yana kula da ita yana tausaya mata komai ya sayo ita komai take so zaiyi mata amma yanxu idan xaiyi shekara guda cur bai ganta ba bazai tambayi Ina take ko meya sameta ba ko kallonta baison yi idan ta gaisar dashi baya amsawa tuna hakan yasa ta fashe da kuka domin batasan me Aiman yake fad'a mata ba tsabar tunanin datai zurfi a ciki ba zato sai gani yayi tana kuka ransa ne yai mugun 'baci yasan yarinyar nan tana cikin matsananciyar damuwa wacce idan bai tsaya tsayin daka ya magance mata ita ba tabbas akwai babbar damuwa huci mai zafi ya fitar yana mi'kewa muryarsa babu yanayin dad'i yace. "Tashi ki d'auko hijab d'inki muje gida gurin Aunty Umma" goge hawayen tai tana mi'kewa ta shiga toilet ta wanke fuskarta dan kada mahaifiyar Aiman d'in ta tambayi kukan me take amma duk da haka idonta yayi ja fitowa tai ganin baya parlon ya fita yasa ta sauya kaya ta d'auko hijab ta fito baya main parlor ma wucewa tai zuwa harabar gida acan ta ganshi tsaye karasawa tai tana cewa "ya Aiman na shirya" "ok muje" gaba ta wuce yana bin bayanta suka fita daga gidan yasa a ransa daga yau bazata sake kwana a cikin gidan nan ba gara ta koma gidansu gurin mahaifiyar sa ta zauna tare da 'kannansa hakan zaifi mata zaman lafiya amma kullum yarinya tana fama da shan wahala sai karewa take kamar kud'in guzuri ya bari Daddy ya dawo zai zo ya fad'a masa sannan zai d'ebe kayanta kaf ya mayar gidansu koda marmari Ayrah bazata sake shigowa nan ba saidai idan sabon aure Daddy yayi ko kuma hankalinsa ya karkato kanta ya bud'e baki ya nemeta da kansa idan ko ba haka ba Ayrah tayi sallama da zaman gidansa har abada saboda halin Hajiya Khubura da na 'ya'yanta suna neman hallaka masa 'ya da azabarsu batare daya sani ba.................. ✍️MRS ÄL'ÄMËËÑ ÄHMÄD ÇË. See you tomorrow morning at 10:50 insha Allah tnks for ur supports masoya nagode da kauna godiya sosai sosai godiya 🌺. Manzon Allah saw Ya shugaban halitta kowa yana a kwance Kaine tsayayye Ya ashja'ul kalki Mustapha ai waninka ne tauyayye Dakai na dogara nake tarewa kaidi na aljani harda maye Dole su ganni tilas su barni dominka ya aba zamzamiyyah. Saleem Musa Abubakar Naja'at Musa Abubakar Fatima Musa Abubakar Aishat Musa Abubakar Abubakar Musa Abubakar I know everything about you is so good but one thing is wrong that you are not mind wannan haka yake ubangiji Allah ya kara had'a kanmu Allah ya bamu zuriya dayyiba Amin. TYPING📲Sat Mar 15/25 10:50AM YUSRAH MUSA ABUBAKAR ✨ ✨. 👑 ROYALTY 👑 In the name of Allah the must benefits and the must merciful ALLAH THE MOST HIGH DOESN'T SLEEP ALLAH THE MOST HIGH IS PURE HE ACCEPT ONLY WHAT IS PURE we love our NABI MUHAMMAD SAW no success without him he's the mirror of our life he's the light of every darkness he've no limits ya rasulullah muna sonka fiye darai da iyaye da dukiya muna sonka fiye da dukka muradi na zuciya ANNABI mu mu ganka shine buri na zuciya lamince mu ganka ya mai salsabil da khausara. 5~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Da'inah. @YUSRAHMS CE Page 09 & 10 Sakamakon komawa da Ahmad zaiyi kamar yadda ya saba idan zai tafi zaibi 'yan uwa yakai musu ziyara hakan yasa ana gobe zai tafi suka shirya shida prince Hamid suka tafi dangin Momy zasu gaishesu a 'ka'ida sai sunje ko'ina karshe suke zuwa gurin 'kanwar Momy saboda suna dad'ewa a gunta tana zaune tare da d'anta saurayi a parlor suna hira ta gansu sun shigo kamar a mafarki musamman Ahmad take bi da kallo domin ya dad'e baizo gida ba kusan shekara biyar shiyasa lokacin daya dawo yaga yadda Baby da Khairat sukai girma yayita mamaki wai 'yan yaran nan ne sukai wannan girman balle yanzu da itama a nata 6angaren take mamakin ganin yadda shima Ahmad d'in ya qara cika mata ido har suka zauna bata daina kallonsa ba saida suka gaida ita sannan ta amsa da murmushi akan fuskarta tace. "Ahmad wai kaine haka kamar kana shan yis"?. Murmushi prince Hamid yayi shima yana kallon Ahmad d'in yace "ai Mama Ahmad aikin sojan nan ya kar'beshi kalli fa yadda yake wani irin 'kyalli ga 'kiba har aje tumbi yake kamar irin manyan alhazawan nan" ya karasa maganar yana sakin dariya ganin wani kallo da Ahmad yayi masa itama mama dariyar tai tana cewa "kai Abdul-Hamid akwai ka da tsokana ina wani tumbi a jikin Ahmad kawai dai kace yayi 'kiba shine". "Eh Mama ai hakan nake nufi kalli fa wuyansa kamar goyayyan bujimi😁". "To ko goyayyan bujimin ne"? Ahmad ya tambaya yana had'e rai kad'a kai prince Hamid yayi yana cewa "oho waya sani ko goyayyan bujimin ne amma da alama shi d'in ne tunda harka tambaya Mama ya kike ya gida kwana da yawa nima bana samun lokaci nazo kullum muna hospital". "Ina lafiya kalau Abdul-Hamid ya wajen Aunty take fatan itama tana lafiya"?. "Lafiyarta kalau tace ma a gaisheki" ya fad'a yana mayar da hankalinsa kan Amaan yace "kai kuma yau kaine abokin taya zancen kenan ina sauran yaran suke Maryam da Humairah". "Humairah tana school sai la'asar zata dawo nine na kaita Maryam kuma taje gidan kanwar Abban mu maybe ta kusa dawowa domin ta dad'e da tafiya". "Ok amma kai bakaje gurin aiki ba"?. "Ina hutu ne" Amaan ya fad'a cikin tsokana "oh hutu kake kamar wani ango"?. "Fad'a 6atawa auren zanyi kwanan nan". "Da gaske"?. "Eh man tunda ku manyan yayu kun'ki yi mu saimu rigaku ai kuma tambayi Mama kaji aure zanyi ni". "Wai haka ne abinda ya fad'a Mama"? Prince Hamid ya tambaya cikin kokwanto kai Mama ta girgiza tana cewa "a'a bansan zancen ba idan ma yana da ita ko auren zaiyi ban sani ba saidai da wasu yayi shawara" kallon Amaan dake 6oye dariyarsa yayi yana cewa "wato son auren kake kenan"?.. "To wa yake 'kinsa baka fad'a min kai yaushe zakai ba"? Kai prince Hamid ya girgiza yana cewa "nikam da sauran lokaci saidai Ahmad yanzu shine a online bani ba domin ni ko budurwa bani da ita". "Au Ahmad d'in aure zaiyi amma ban sani ba"? Mama ta tambaya tana kallon sa kaiya girgiza mata yanaiwa prince Hamid kallon kana shiga safgata fa kafin yace "ni ba aure zanyi ba kawai dan yaji dad'in bakinsa ya fad'a niban tashi yin aure ba sai gaba sosai" yana rufe baki prince Hamid yace "ji 'karya ba wani nan malam ka daina wani wayancewa ka fad'a musu gaskiya". "Ai gaskiyar na fad'a musu" a she'ke prince Hamid yace "a hakan"?. "Kwarai a haka d'in". Tashi Mama tai tana kawo musu abun sha sannan tace "Ahmad Abdul-Hamid yace aure zakai dama kana da budurwar ne bamu sani ba"? Kaiya girgiza yana cewa "nifa Mama ba aure zanyi ba kawai ya fad'a ne" sauke ajiyar zuciya Mama tai tana hamdala a ranta harda sakin murmushi tana jinjina kai tace "yauwa fa Ashe wasa yake aina d'auka da gaske ne Allah ya kaimu Allah ya kawo mace ta gari musha biki tunda mune iyaye" ta fad'a tana hasko wani abu a ranta dan tunda dad'ewa take fata da son a cikin yaranta Maryam ko Humairah wani ya samu ya auri d'aya a cikin Ahmad ko prince Hamid yanzu kuma take jin batun Ahmad zaiyi aure shine taji hankalinta ya tashi saida yace bayi zaiyi ba taji dad'i har mantawa tai da suna hira tsabar tunanin data tafi iya su uku ne suke zancen su sun dad'e a gidan daga baya suka mi'ke zasu tafi tare da aje mata kud'i da atampha kamar yadda suka saba duk lokacin da suka xo mata cikin jin dad'i tayi musu godiya tare da Amaan suka mi'ke shima zai fita daga gidan sukai harabar gida acan ma saida suka sake tsayawa sukai hira sosai sannan sukai mai sallama suna shiga motar da suka zo da ita shima da yake fita zaiyi tasa motar ya nufa daidai an bud'e gate d'in motar Maryam ta shigo su kuma sun fita da mamaki ta bisu da kallo domin kafin Ahmad ya d'aga glass d'in ya rufe ta ganshi da sauri ta Parker ta fito amma sunyi nisan da ko hannu ta d'aga bazasu ganota ba ha'kura tai ta shiga gidan ganin Mama zaune a parlor ga kud'i a gabanta da atampha zama tai tana kallon kayan tace. "Mama wa nake gani kamar Ahmad ne yazo gidan nan ko yanxu suka fita dama ya dawo ban sani ba"? Kai Mama ta d'aga tana cewa "eh shine tare suke da Abdul-Hamid yanzu suka fita baki had'u dasu ba a harabar gidan saboda na le'ka naga suna tsaye da Amaan"? Kai Maryam ta girgiza tana cewa "Bamu had'u ba na shigo sun fita kuma da yake Ahmad yana da gudu a mota kafin na fito na d'aga musu hannu sunyi nisa amma naso mu had'u wallahi nifa Mama haka kawai nake jin ina son Ahmad d'in nan amma shi babu ruwansa dani ko gaisuwar arziki bata shiga tsakanin mu taya zan samu harya karkato da hankalinsa kaina mu saba ya kamu da sona nidai ina sonsa wallahi" kallonta sosai Mama tai tana cewa "kina son Ahmad kikace Maryam"? Kai Maryam ta d'aga tana cewa "eh gaskiya ina sonsa Mama da ace zai amince ya aureni zanyi farin cikin da ban ta'ba yiba" Maryam na rufe baki Mama tai murmushi tana jinjina kai ta kalleta tana cewa. "Maryam ni kaina ina so d'aya daga cikinku ya auri Ahmad ko Abdul-Hamid ina so nima naga hakan ta faru haka kawai nake jin ina son hakan shiyasa yanzu da Abdul-Hamid yake cewa wai Ahmad d'in aure zaiyi bakiji yadda naji gabana ya fad'i b......................... Bata bari Mama ta karasa ba a zabure ta zaro ido tana cewa "aure zaiyi kuma na shiga uku"? Kai Mama ta girgiza tana kallon yadda lokaci guda Maryam d'in ta burkice tace "a'a ba aure zaiyi ba ashe wasa Abdul-Hamid d'in yake dan yaji me Ahmad zaice ne gashi gobe zai tafi da kamar ace bai dad'e da dawowa ba wallahi kayanki zaki tattara kije musu ko sati biyu kiyi ki samu ki ja hankalinsa ki ri'ka shishshige masa ta yadda ko baya sonki ko bai fahimci kina sonsa ba daga baya ya gane kema ya soki" gyara zama Maryam tai tana cewa. "Allah Mama". "Allah kuwa da gaske Maryam zan tayaki indai kina sonsa zan samu Aunty nayi mata maganar in yaso ta sameshi ta fad'a masa Allah yasa ya amince zai aureki" da sauri Maryam ta d'aga hannu tana cewa "Amin ya Allah Mama wallahi nima haka nake fata wani lokacin har mafarki nake ya aureni muna tare" murmushi Mama tai tana cewa "humm kamar yaune insha Allahu zai aureki ya zauna dake idan akai masa tayi bazaice a'a ba zai yarda nasan muddin Aunty ce ta fad'a masa bazai musa taba kawai kisa a ranki kamar kin aure shine kin zauna dashi ina so kawai naga na had'a jini da 'yan sarauta a rayuwa kamar yadda Aunty Allah ya d'agata ta lokaci guda Aliyuddeen ya ganta nima naso ace Ashraf 'kaninsa ya yarda ya aureni amma ya'ki aurena har jinya saida nayi na dad'e a asibiti banyi tunanin zan warke har nayi doguwar rayuwa haka ba kwatsam muka had'u da Abban ku shikenan na ha'kura da Ashraf hankali na ya dawo kansa kema inai miki fatan ki taki sa'a irinta Aunty Ahmad ya soki ya aureki tunda dai kinji baida budurwa dagewa zaki idan ya sake zuwa gida kije duk wata hanyar da kikasan zaki burgeshi ita zaki bi kinji"? Kai Maryam ta jinjina tana sakin murmushi tace "Allah ya Allah ubangiji kana gani kana ji ya mahaliccin samai da 'kassai ina ro'konka ka cika min burina akan bawanka Allah ka lamince min ka 'kaddara Ahmad shine mijina wanda zanyi rayuwa mai cike da inganci dashi" tana rufe baki harda Mama wajen tayata cewa "Allah Amin Amin in Allah yaso Maryam ke matar Ahmad ce sai kin aureshi ki kwantar da hankalinki tunda muna da ala'ka dashi hakan bazai zama abu mai wuya a gurin muba" fuskar Maryam cike da annuri tace "shikenan Mama Allah ya tabbatar da abinda kika fad'a bari naje nayi wanka dan na d'ebo rana wannan anguwar da naje kawai saboda naga Ahmad hankalina ya fita daga jikina yasa banji zafin ba sai yanzu" ta fad'a tana mi'kewa da niyyar idan tayi wanka saita fito taci abinci domin 'karfe d'aya da rabi tayi tana barin parlon Mama data bita da kallo ta sauke daddad'an numfashi tana cewa "ubangijin rahma ya amsa mana addu'ar mu Allah yasa Maryam ta dalilin ki mafarki na ya zama gaskiya ki auri Ahmad da ranar nayi rawa na qara nayi farin ciki nai gud'a nai shewa a gaban kowa Allah ya kaimu da alkhairi" ta karasa maganar tana tashi itama ta shiga bedroom. Ahmad kam suna komawa gida part d'in Momy suka shiga babu kowa daga Baby sai Khairat domin yau basu je school da safe ba sai karfe hud'u zasuje lecture shima ba dad'ewa zasuyi ba suna zaune a dinning ya shigo bayansa prince Hamid Baby ce ta fara ganinsa ta d'ebo abinci a spoon zata kai baki suka had'a ido da sauri ta janye nata tana fad'in "innalillahi wayyo Allah dama Yaya Ahmad ba nisa yayi ba..................... Bata gama tunanin da take ba taji saukar muryasa yace "ku sauka a dinning d'in nan" da sauri ta dawo nutsuwarta zuciyarta ta harbawa ganin har lokacin ita yake kallo da sauri ta mi'ke zata bar gurin kujerar data tashi ya zauna yana cewa "ke dawo nan ina zakije wannan sauran jagwalgwalon da kika bari waye zai cinye miki shi" tsayawa tai tare da juyowa ta dawo zata dauka yace. "Serve me" d'auke numfashi tai na wani lokaci kafin da'kyar muryarta na kokarin fara rawa tace "me zan saka maka"? Bai d'ago ba baiyi magana ba ta d'auka ko baiji bane saboda akwai Bluetooth a kunnensa saida ta sake maimaitawa sannan ya d'ago yayi mata kallon minti biyu kafin ya sake cewa. "Serve me" tun batai motsi ba prince Hamid dake zaune a d'aya daga cikin kujerun dinning shima har Khairat tayi serving d'insa tabar gurin ganin yana neman wahalar da ita gashi bai bari ta gama cin abincin yadda zaibi jikinta ba yace "kaga malam ba'a ciki da mugunta tai serving d'inka me? Ta tambayeka me kake so ka sake cewa wata uwa tai serving d'inka" mayar da kallonsa kan Baby yayi yana cewa "kinga Baby rabu dashi saka masa duk abinda kikaga dama ki tafiyarki kije ki karasa cin abincin ki yabi jikinki" jin abinda prince Hamid yace yasa Baby tad'an saci kallon Ahmad taga sam ba inda take yake kallo ba hankalinsa nakan waya shawarar prince Hamid tabi kawai ta bud'e dishes tai serving d'insa abinda itama ta za'ba taci ta d'auka zaice a'a ta sauya masa sai taji baiyi magana ba hamdala tai a ranta cikin azama kuwa tabar gurin ta koma tayi bedroom domin can taga Khairat ta nufa bayan sun tashi. Prince Hamid saida ya bari Babyn ta wuce ya kalli Ahmad yana cewa "amma kai kam bansan ranar da zaka canza ba Ähmäd ba yanzu ne lokacin da zakaji takaici ba sai gaba irin wannan had'e ran da kake mata ya kamata ka daina kullum ina tunatar maka ita ka za'ba matsayin abokiyar rayuwarka wacce kake sa ran da ita zakai rayuwar aure amma baka da wacce zaka ri'ka yiwa muzurai sai ita kasan cewa kuskure kake aikatawa kuwa"? Kai Ahmad ya kad'a yana cewa "yanzu bani da lokacinka ka bari zuwa dare zan nemeka domin bana gane abinda kake fad'a yanzun" kai prince Hamid ya jinjina yana cewa "ok kada Allah yasa a gane akwai ranar ganewar tana nan zuwa indai baka canza ba" yana rufe baki Momy ta fito ganin basu Baby ba alamarsu ta kalli su Ähmäd da suke zaune tace. "Abdul-Hamid kun dawo kenan ya kuka barosu fatan duk kowa yana lafiya"?.. "Eh Momy duka suna lafiya suma suna gaida ke kuma suna godiya". "Ok ina Khairat da Baby suke kohar sun gama cin abincin ne"? Kai prince Hamid ya girgiza yana cewa "a'a ga mugun daya kore su nan suna bedroom d'insu" "tofa bedroom kuma haba Ähmäd daka 'kyale su kujeru nawa ne a dinning basai kace su koma gefe ba amma saika kora min yaran cikin bedroom" d'agowa Ahmad yai yana kallon ta yace "haba Momy ina kan dinning suma suna kai saboda kafad'a ta d'aya take da tasu tab aiko da sunci duka". Kai Momy ta girgiza tana cewa "tsiya ta dakai Ahmad mugunta meye abun cin dukan dan kawai kana kan dinning suma suna kai ba 'kannin ka bane"?. "Kannai nane Momy amma bana so su rika ganin damata kamar yadda suke ganin sau'kin halin Abdul-Hamid shiyasa suka raina shi nikam basu isa ba ko kallo nayi musu sun sani" murmushi Momy tai tana kallon sa da abinda yake fad'a kafin ta jinjina kai tana komawa ainishin parlon ta zauna tunda tasan me hali baya fasa halinsa a haka ya taso tun suna yara ma ba sau'ki 'ya'yan bayi ma sunci duka sosai kusan kullum sai ya daki yara sama da biyar hud'u uku har gajiya Momy tai tun tana fad'an ta ha'kura saida yayi hankali kuma ya daina kowa ya huta su Khairat kuma suka hau layi su kuwa idan ba aure sukai ba babu ta yadda za'ai ya daina horasu. Khairat tana zaune taga Baby ta shiga da sauri da plate a hannunta zama tai tana sau'ke numfashi tace "kai jama'a gaskiya ya Ahmad yana da wuyar sha'ani wannan matarsa ta banu da tsiri" dariya Khairat tai tana gyara zama ta kalli Baby data bud'e plate d'in data shigo dashi taci gaba dacin abincin tace "humm ai naso na tsaya naga yadda diramar zata kasance saidai da yake na gama hadawa ya Hamid nasa kuma idan na tsaya boss zai iya cewa na tsaya gulma yasa na taho naso ace naga yaya kuka 'kare" baby data kai lomar abinci tace "ya muka 'kare kuwa tambayar sa nayi abinda zanyi serving d'insa bazai fad'a ba saidai ya sake cewa serve me kiji dan Allah" sabuwar dariya Khairat ta kumayi tana cewa. "Ai ya Ahmad humm nifa harna matsu gobe tayi ya tattara ya koma mu huta". "Duk matsuwarki Aunty Khairat baki kaini ba kawai dan babu yadda zanyi ne ai inaga gobe sai mun had'a party wallahi bayan ya tafi" murmushi Khairat tai cikin tsokana tace "wai inama ace wannan maganar da muke yana jinmu tabd'i da azabar da zamu sha kafirin dake qabari ma saiya fimu samu nutsuwa" daina cin abincin Baby tai tana ture plate d'in tace. "Wallahi Aunty Khairat har kinsa abincin nan ya fita a kaina da kikace inama ace yana jinmu haba yanxu ace ya Ahmad yana jin wadannan maganganun da muke akansa ai yau kam saidai muyi kwanan asibiti dan bana tunanin zamuje gobe a hayyacin mu". "Garama ki karasa cin abincin ki ba jinmu yake ba balle yad'au matakin daya saba hum gaskiya gayen nan yana garamu" mi'kewa Baby tai tana cewa "nikam abincin nan ya gama fita a kaina barima kiga na tashi wanka zanyi kawai na shirya kamata yayi ace kafin mu tafi lecture d'in nan mu le'ka Sultana Addah" ta fad'a tana shiga toilet Khairat tana zaune wayarta tahau ringtone ganin me Kiran yasa ta gyara zamanta tana d'auka ta kashe muryar suka fara waya Baby na jinta saida ta gama ta fito ta kalli Khairat tana jinjina kai kafin ta saki murmushi tana cewa "kaga masoyan asali" hararar ta Khairat tai tana cewa "kajita ko wai Baby ce maicewa kaga masoyan asali" zaro ido Baby tai tana cewa "a'a Aunty Khairat yada haka kinsan ya Shadad bashi da mantuwa so kike a ranar daya dawo ya kar'be ni da kamun kunne ko"? Khairat bata kula taba sai wayar data mi'ko mata tana murmushi tace. "Yace ki kar'ba ai banice na had'a ku ba dama yana jinki". Kar'ba Baby tai tana karawa a kunne tace "hello Yaya ina yini"? daga 6angaren Shadad yace "wato Baby kin raina Khairat ko ashe dama bayan tahowata haka kike mata"? Zaro ido Baby tai tana girgiza kai kamar tana gabansa tace "wallahi Yaya ina bata girmanta yanzun ma tsokanar ta kawai nake yi bada wani abu nace hakan ba". "Ok yayi ya kike ya karatu fatan kina dagewa"?. "Eh sosai Yaya ina kokari kuma ka tambayi Abban mu kaji". "No basai na tambaye shiba ai ina tambayar Ahmad duk wani abinda kuke yi kuma yana fad'a min idan yabar gida saina dawo tambayar Abdul-Hamid" had'a ido Khairat da Baby sukai suna jinjina kai oh wato dama ashe baya nan ma yana tambayar ya suke suna karatu ko a'a da yake Baby tana d'an sakewa dashi ba kamar Ahmad ba tace "ya Shadad me ya Ahmad yace maka daka tambayi muna karatu ko bamayi"?. "Ina ruwanki da amsar daya bani baiwa sweetheart wayar nagama dake" dariya tai tana mi'kawa Khairat wayar ta wuce gaban mirror Khairat na kar'ba tace "nimafa ta Babyn me ya Ahmad d'in yace maka dan naji hankali na bai kwanta ba". "Wani abu yace min aida ya fad'i cewa bakwa mayar da hankali zaki sani saboda da yanzu na kira wayarki na muku fad'a amma hakan ma tunda gobe zai tafi zansa Abdul-Hamid ya d'ora inda Ahmad d'in ya tsaya kafin na dawo" murmushi Khairat tai tana cewa "ai kuma ya Hamid bashi da fad'a irin naku koka wakilta shi babu abinda zaiyi mana". "Dama badan yayi muku wani abu zan wakilta shiba a'a kawai ni damuwata ya kula da karatun ku shine kawai" "Ok nagane aikuma muna karatun sosai kuma ko Abban mu ka tambaya". "Basai na tambaye shiba komai ina sani zan kiraki zuwa jimawa yanzu ina da uzuri". "To muma dama gurin Sultana Addah zamuje". "Yayi idan kunje ki kirana ina son zanyi magana da ita ta wayarki". "Ok zan kiraka ba dad'ewa zamuyi acan ba muna lecture karfe hud'u da rabi nida Baby". "Ok karki manta ki kira"?. "Tom zan kiraka bye" ta fad'a tana katse kiran kai Baby dake zaune ta girgiza kai tana juyowa ta kalli Khairat sai kawai taji dariya tazo mata murmushi ta saki tana mi'kewa tace "lallai Aunty Khairat me masoyi wato ke auren had'i kike so"? Kai Khairat ta jinjina tana cewa "kwarai auren gida nake so tunda ina son wanda zan aura ai ba wata damuwa ko kema shi kike so kiyi"? Khairat ta tambaye ta cike da tsokana ba arziki kuwa tasa Baby da sauri ta girgiza kai harda zaro ido kamar wanda Khairat d'in ta fad'a mata abun firgici tace "wayyo Allah Aunty Khairat dan Allah ki rufa min asiri kar wani ya jiki" hhhhh dariya Khairat tai tana cewa "ba wanda yai mana la6e iya mune anan part d'in kawai kedai tsoron kine na gado da kika saba amma Baby meyasa ke bakya son auren gida yana da dad'i fa kuma ki gwada kema zaki gani" Khairat ta karasa maganar tana she'kewa da dariya ganin yadda tasa Babyn ta sake 'kwalalo ido waje tana cewa "tabd'ijan nikam saidai nace Allah ya tsari gatari da saran shuka wallahi ko kad'an bana son auren gida". "Kuma idan wani a cikin su ya Ahmad d'in yace yana sonki fa tsakanin shi da ya Hamid nan kuma ya zakiyi"? Dafe 'kirji Baby tai tana cewa "a'uzubillahi subahanallahi innalillahi wa inna ilaihi raji'un Allah karya nuna min wannan ranar tashin hankalin bana fatan hakan ya zama gaskiya ko a mafarki haba Aunty Khairat kinji yadda kikasa zuciyata ta buga kuwa"? Dariya Khairat tai tana cewa. "Uhmm Baby kenan nima dama na fad'a ne dan na gwada ki amma koni bazan so ki auri ya Ahmad ba saboda gaskiya auren ya Ähmäd sai mace mai mugun ha'kuri domin yana da wuyar sha'ani wallahi". "To kin gani Aunty Khairat nikuwa me nake kallo zan yarda na amince zaman aure da ya Ahmad habawa ya Ahmad fa jama'a heyyy tabd'ijan uhmm bari kawai nayi shiru Allah ya kiyaye" murmushi Khairat tai ganin yadda ta caza Babyn yasa tace. "Uhmm ai dazaki aure shi mukam 'yan shan biki ne da yin anko ashobi zamuyi masu kyau mu kama Hall me tsada mu gwangwaje ranar auren nan". Kai baby ta jinjina tana cewa "wai harna haskoni a misali yau ranace ta fito na zama matar ya Ahmad kan bala'i ai wallahi Aunty Khairat dana auri ya Ahmad gara na auri almajiri wanda saiyi fita bara ya samo mana abincin da zamuci" Dariyar daba shiri Khairat tai tana kallon Baby wacce tai maganar tsakaninta da Allah abinda ke ranta ta fad'a tace "Kai Baby lallai kin d'auko da zafi wannan da ya Ahmad zaiji tabd'ijan dakuwa zaki yabawa aya za'kinta wallahi dan banga me ceton ki a hannunsa ba kuma maybe karshen wasan ya aureki d'in yaga ya zaki"? Ta'be baki Baby tai tana cewa tace. "Humm Aunty Khairat daina fad'a kar wasa ya zama gaskiya nikam bana fata idan iya dukana zaiyi da sau'ki d'aya kenan ai a misali yaji nace dana aureshi gara na auri almajiri kuturun ubancan wallahi inaga farfesu na zaiyi duka kuwa saiya sa wannan jikin nawa ya zama kamar gwanda tsabar nuna shin da zaiyi kawai Aunty Khairat mubar wannan wasan 'kwai'kwayon please kije kiyi wanka mu tafi kar lokaci ya qure mana". Mi'kewa Khairat tai tana cewa "aiko dai kinyi gaskiya dan wannan maganar tawa tayi kama da tatsuniya bari nazo muje kinga ma maganar da muke naso sha'afa sweetheart yace idan munje nai kiransa zaiyi magana da Addah" ta fad'a tana wucewa da kallo Baby tabi bayanta tana murmushi wato ita kuma auren gida take so "humm ya Shadad d'an uwan ya Ahmad wajen zafin rai da iya dila mutum" ta karasa maganar tana sau'ke numfashi har taso 'kwaruwa musamman tuna cewa da Khairat tai wai ko Ahmad ya aureta kamar sake maimaita maganar akai haka ta zabura tana girgiza kai tace "ina wannan fad'a ce kawai auren gida for me never Allah ya kiyaye min wannan 'kaddarar ta sameni" saboda ta daina tunanin maganar da sukai ma yasa ta d'auko littafin da Ahmad ya bata ta bud'e tana dubawa kafin Khairat d'in ta fito su tafi.......................... MRS ÄL'ÄMËËÑ ÄHMÄD ÇË 🌹. Manzon Allah Saw Aminci ga muftahul jannatun naimah Aminci ga kiblar bayi a ran qiyama Aminci ga Mai shiryarwa cikin salama Aminci ga duk Mai matsayi dakai ya samu Aminci ga duk Mai girma dakai ya samu Aminci ga duk Mai daraja dakai ya samu Aminci ga fatuhul Akbar aya imamu Yusrah Musa ce tare dani da gaisuwa ta🙏 Ka tausayawa zuciyata naganka ko sau d'aya a rayuwata. Thanks for ur supports 🔥 nagode masoya ana tare insha Allah. TYPING📲YMA DUTSE NEW WORLD 🌏 YUSRAH MUSA ABUBAKAR ✨✨💯. 👑 Royalty 👑 A*W*A ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫 Home of hospitality and harmony gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan ta haka taken mu yake tafiyar mu babu rago babu maci amana tsantsan gaskiya muke nunawa. STORY WRITTEN ND EDITING ✍️ YUSRAH MUSA ABUBAKAR Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë 🌺. 6~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Taibanah. Bismilllahir Rahmanur Rahim 📿 @YUSRAHMS CE Page 11 & 12 Tsabar yadda Baby tasa tafiyar Ahmad a ranta har mafarki tai wai ya tafi kuma harda su a rakiya saida asuba bayan sunyi sallah sunyi karatu Baby ta kalli Khairat dake shirin komawa ta kwanta duk da gari yayi haske sosai tace "Aunty Khairat kinsan wani abu? Kai Khairat ta girgiza tana kallon ta itama taji wanne irin mafarki tai harda tashi zaune tana gyara zama tace "ina jinki wanne irin mafarki kikai"? Kai Baby ta jinjina tana cewa "uhm inji me ciwon baki abun ba'a magana waifa mafarki nayi wai ya Ähmäd ya tashi tafiya mune 'yan rakiya" d'an zaro ido Khairat tai tana sakin dariya tace "tabd'ijan ahh dole kice ba'a magana wannan lamari yafi karfin mu wane mu" mi'kewa Baby tai tana cire hijab d'in jikinta ta aje tana cewa "um gane min hanya Aunty Khairat indai ba mu 'ka'kalowa kanmu dukan ban kwana ba mezai kaimu inda ya Ahmad yake randa zai tafi musamman idan ya sako kayan soldier d'in nan nasa wani irin kwarjini yake ko daga nesa na hangoshi da gudu nake 6uya kamar naga abun cutarwa haba gaskiya ya Ahmad yana lokaci muna shan kallo yau dai zamu huta please Aunty Khairat karki manta da partyn da zamuyi" Baby na rufe baki cikin tsokana Khairat tace. "To zamuyi party amma saidai yanzu muje muyi masa sallama". "Wa zamuyi wa sallama amma dai ba ya Ahmad ba"?. "Shi mana ba shine zaibar masarautar ba". "Amma da wasa kike Aunty Khairat mune zamuje yiwa ya Ahmad sallama aiko daya sallamar damu". "No babu abinda zaiyi mana shima yau yana busy bazai bi takanmu ba tashi ma muje maybe muyi masa rakiya damu". "Dawa za'ai rakiyar? Amma bada niba wallahi bazanje ba nida ya Ahmad saidai idan ya dawo na ganshi amma banda yau". "Idan baki tashi munje ba baza muyi partyn ba" Khairat ta fad'a da serious face kamar gaske ta d'auka Babyn idan taji haka zatace suje sai taga ta kwanta a kusa da ita tana cewa "a fasa kawai indai sai naje gurin ya Ahmad da muyi kawai a barshi yafi" dariya Khairat tai tana cewa "humm ai baki iyaba Baby da kince ni d'in naje ni kad'ai nima fa ba iya zuwa zanyi ba kawai Ina tsokanarki ne ban fad'a miki ba tun a jiya ya Shadad ya turo min kud'in da zamuyi partyn dashi amma baisan partyn murnar tafiyar ya Ahmad bane 'karya na sharara masa ya turo min" baby dake lullu'be tace. "Oh kice zamuyi kenan"?. "Kwari zamuyi dan tun a jiyan na baiwa ya Hamid kud'in na fad'a masa abubuwan dazai sayo mana idan ya fita kinsan mu baza'a barmu muje ko'ina ba daga school sai gida". Tashi zaune Baby tai tana cewa "amma gari fa ya waye haske ya fito sosai nasan maybe yanzu ai ya tafi mu tashi mu tafi part d'in Momy nifa yau da yunwa na tashi domin jiya da dare banci abinci ba iya fab-choculate d'in nan naci dan Allah Aunty Khairat tashi muje amma idan zamu shiga mu tsaya mu saurara tukuna kar muje mu fad'a muga Yaya boss" tashi Khairat tai tana dariya tace "tab kina fad'ar haka na hasko wata mugunta ace muna zuwa kofar parlon Momy kin bud'e zaki shiga ni kuma na turaki ciki da 'karfi kuma ace ya Ahmad d'in yana parlon a zaune" bud'e baki da ido Baby tai tana komawa ta bayan Khairat tace "please kar kiyi haka indai ba so kike yau nayi wunin zazza'bin wahala". "Ai dama bayi nace zanyi ba misali nayi miki". "Misalin jinsa nayi kamar gaske shiyasa nima nace haka" daidai sun karasa bakin kofar part d'in Momy basu shiga ba saida suka tambayi masu tsaron kofar ko Ahmad yana ciki sukai musu albishir cewa shikam tun asuba yabar masarautar nan prince Hamid ne yayi masa rakiya jin wannan daddad'an labarin yasa da gudu suka bud'e kofar suna shiga ko jira a bud'e musu basuyi ba Momy tana zaune ita kad'ai sai gani tai sun fad'a mata da gudu suna zama suka saka ta a tsakiya kowa na fitar da huci da mamaki take kallonsu da ace Ahmad yana nan sai tace ko shine ya korosu suke irin wannan gudun tashin hankalin to yanxu kuma da baya nan lafiyarsu kalau kuwa.............. Katse mata tunani Khairat tai har lokacin numfashinta bai dawo daidai ba tace "Momy ya Ahmad ya tafi ne ko yana nan"? Tun kafin Momy ta bata amsa Baby tace "Momy wai ya tafi inji securities d'in dake tsaye a bakin kofar part din nan haka ne"? Murmushi tai tana kallon su tad'an girgiza kai tana cewa "ok shine dalilin da yasa kuka shigo a haukace saboda kunsan me gyara ku baya nan ko"? Daidaita numfashi Baby tai tana cewa "da alama ya tafi kenan Momy"?. "Eh ya tafi ko wani abu zaku bashi irin wannan nema haka nasan idan yana nan ba haka kuke ba yau kuma saboda kun tabbatar baya nan shine kuke tambayar sa"?. Kai Khairat ta girgiza tana cewa "a'a Momy ba haka bane kawai dai mun tambaya ne amma tunda ya tafi munji dahir masha Allah da sau'ki Allah abun godiya sabuwar rayuwa ta dawo heheheee shagaliii yau zamu shana" jinjina kai Baby tai tana cewa. "Humm wallahi yau yadda kika san sallah Aunty Khairat haka nake jin farin ciki har wata sabuwar sansanyar iska ce take ratsa ni da Yaya Ahmad ya fita daga masarautar nan shikenan kuma mun huta kafin ya sake dawowa ya sake sakamu a gaba" murmushi Momy tai tana cewa "wato a gabana kuke farin ciki da tafiyarsa ko? d'ana nefa bakusan yadda ni kuma nake jin kewarsa a raina ba amma kunzo kun sakani a gaba da maganganun ku wannan ai saiku sani kuka" tana rufe baki duk su biyun suka zaro ido da sauri Baby ta girgiza kai tana cewa. "Please Momy kiyi ha'kuri dan Allah ya Ahmad d'in ne ba'a iya masa wallahi muma ba'a son ranmu muke masa hakan ba dole tasa saboda irin hanamu sakewar da yake". "Ai idan ma yana nan ba hanaku sakewa yake ba kune kuke Hana kanku duk tsiya idan bakuyi laifi ba bazai dake kuba". Ha6a Khairat ta ri'ke tana kallon Momy tace "Eh haka ne Momy amma wallahi ba mu bane muke hana kanmu ba muna son mu ri'ka wargi baya barinmu saidai yazo ya tsare gida yadda motsin kirki bazaka iya yi ba yayita muzurai yana hahhad'e rai wai shi ala dole soja haba jama'a wannan matarsa zata sha wahala indai akace itama irin takurar mu zai nuna mata". "Kwarai Aunty Khairat idan yace d'auko min ruwa me sanyi saita d'auko tun kafin ta karaso zaice bamai sanyi ba ta mayar ta d'auko masa d'an tsakatsaki ko marar sanyi dan naga alama ya Ahmad koba nefa caji yake yanzu zaisa mutum yai shokin da tashin hankalinsa" Baby ta fad'a tana maida fuskarta kalar tausayi dariya Momy tai tana cewa. "Lallai wato saboda kunga baya nan yayi nisan kiwo shine kuka zauna kuka kafa gulmarsa ko aiko indai mukai waya saina fad'a masa duk abinda kuka fad'a a kansa har qari sai nayi". Yarfa hannu Baby tai tana ri'ko hannun Momy tace "Innalillahi dan Allah Momy karki fad'a so kike ya d'auki hutu saboda mu akan wannan maganar ya dawo gida yaci ubanmu ya koma kenan" kai Momy ta girgiza tana murmushi tace "a'a bazai dawo gida ba saboda daku saidai tunda ba nisa yayi ba zaisa a saka masa ku mota a kaiku inda yake yaci 'kaniyarku acan son ransa sannan yasa a d'auko ku a dawo daku gida" Momy na rufe baki Baby tace "a wuce damu asibiti dai ya Ahmad d'in ne zaisa a kaimu har inda yake kuma hukunci zai bamu harmu dawo mu samu damar iya cigaba da rayuwa batare da munga likita ba tab uhmm Allah dai ya rufa mana asiri. "Amin Khairat tace tana cigaba da cewa "ai Baby ko zamu samu d'an hutu da sassauci a gidan nan maybe sai yayi aure kila ko muma ma huta dan ko 'ya'yan bayi bazamu fad'awa hutu ba tunda su babu wanda yake takura musu mu kuwa fa kullum kana ankare sai kace wanda kake filin ya'ki Allah yasa daya dawo gida yayi aure kawai a wuce gun". Da sauri Baby ta d'aga hannu tana cewa "Amin ya Allah Aunty Khairat Allah yasa yayi auren nan da wuri indai hakan zaisa hankalin mu ya kwanta aidai dole zai rage matsa mana lamba yana part d'insa zai rage zirga-zirga a gurin Momy da part d'in Mami ta Nan zamuji dad'in abun" dariya Momy tai tana kallon Baby datai maganar kawai ta girgiza kai domin tasan akwai guguwa a gaba duk ranar da Baby ta fahimci Ahmad ita yake so kuma ita zai aura wai za'a kwashi 'yan kallo bata jin hakan zaizo da sau'ki sau'kin d'aya tunda Abban Baby din Sultan Ashraf ya hana yace kada a sanar mata sam a rabu da ita suje a haka iya daga ita sai Khairat sune basu sani ba amma kowa ya sani daga Momyn har Abba da Mami su Sultana Addah da Sultan Sharfaddeen mai martaba duk sun sani................. "Momy" Baby ta fad'a ganin ta fad'a tunani dawo da kallonta Momy tai kan Babyn tana cewa "na'am" "tunanin me kike yi zamuyi breakfast"? Kaita d'aga tana cewa "ok kuje dinning man kuci tunda naga ku bakwa son masu aiki suyi serving d'inku ko meyasa oho" mi'kewa sukai Khairat na cewa "saboda tsaro Momy gara hakan kinga nan gaba a gidan mazajen mu mun riga mun saba da kanmu zamuyi nikam girki ma dan baza'a barni bane da yanzu Ina zuwa kitchen ina ganin yadda akeyi na koya amma duk da hakan alhamdulillah tunda wata rana muna fakar ido mu shiga kitchen d'in Mami mu d'an girka wani abu idan mukai searching muka gani". Basu dad'e da zama a dinning ba prince Hamid ya shigo yana aje musu kayan da Khairat ta fad'a masa ya sayo musu baisan me zasuyi ba yana zaune suna zance da Momy yaga sun fara gyara gurin suna hura balloons suna d'aurewa ga cake da suka aje d'an karami mai kyau anyi masa kwalliya a jiki an rubuta happy valentine day da mamaki ya kalli Khairat yana cewa. "Ummul-khairi wai wannan d'in na mene naga dai yau ba ranar valentine day bane ku kuma na me zakuyi"? Dariya Khairat tai zatai magana Momy tace "murnar tafiyar Ahmad suke shine harda had'a walima a gabana kuma na fad'a musu ni d'ana ne kewar tafiyarsa nake ji kamar nayi kuka su kuwa farin ciki suke gashi nan ka gani har party zasu had'a kuma a gabana" da sabon mamaki prince Hamid ya sake kallonsu jin abinda Momyn ta fad'a yana cewa. "Oh duk wannan murnan tafiyar Ahmad ne lallai kun kyauta amma meyasa bakuyi jiya ba kuka bari sai yau a gabansa ya kamata kuyi ya gani amma kwazo kuna ihu bayan hari mu amfanin me zaiyi mana ko taya ku zamuyi"? Ya tambaya yana kallon dukkan su biyun Baby da take jera grapes da yankakkun Apple red and green tana yiwa cake d'in kwalliya tace. "Yaya Abdul-Hamid murna ta zama dole yau sabuwar rana ce a garemu zamu sha shagali muyi komai muke so babu mai takura mana koda ya Ahmad ne ya dawo yau sai mun gwangwaje yasin" kai prince Hamid ya jinjina yana sakin murmushi yace "anya Baby idan Ahmad yana nan zaku iya yin wannan abun sannan yasan dashi kuke"? Cikin 'kwarin gwiwa Baby tace "kwarai ya Hamid zamuyi" ok kawai abinda yace mata bai sake magana ba Momy tana kallonsa ya zaro wayarsa ya fara daukarsu video batare da sun sani ba murmushi tai tana d'an sakin dariya wato yanxu kuma da zasu d'ago su gani maybe valentine d'in da baza ai ba kenan saidai suyita bada ha'kurin a goge videon murmushi prince Hamid yake yana ta tsokanar su suna magana duk basu san abinda yake ba har suka gama had'awa ganin zasu d'ago yai sauri yai saving yana aje wayar yace. "Wow gaskiya cake d'in nan yayi kyau bari na dau'ki photonsa na d'ora akan DP (difi) d'ina ya fad'a yana d'auko wayarsa ya d'auka yana cewa "wannan valentine d'in ba iya ku kad'ai zakuyi ba harda ni saboda idan yana takura muku nima Ina jin babu dad'i idan kin fara Khairat ko ke ko Baby wata da kirani a waya" yana rufe baki Baby tace "ni ya Hamid bani da waya ya Ahmad ya hana na ri'ke yace sai nayi aure" ta fad'a tana zun6ura baki juyawa yai zai fita yace. "Ok Ummul-khairi ki kirana". "Tom" tace tana mi'kewa ta kalli Baby tana cewa "muje muyo wanka wannan abun dole saida kwalliya ina Sultan please mu kar'bo aron mp d'insa mu gwangwaje da ita". "Mu fara yin wankan tukuna sai muje mu kar'bo maybe bazata wuce tana parlor ya sakata a caji ba dan shima yau ranarsa ce tunda ya boss baya nan muje mu fara shiryawa" wucewa sukai suka bar Momy ita kad'ai a gurin tana kallon yadda suka tsara abun nasu kamar masu yin birthday party a ranta tace "bari sai sun fara zan kira Ahmad video call batare da nayi magana ba yaga yadda ake party da murnar barinsa gida maybe idan yaga haka ya canza ya daina takura musu. Wanka sosai su Khairat suka d'auka sun saka kaya iri d'aya an soke d'aurin kwali anyi makeup kowa da bayyanan nan farin ciki a fuskarta suka fito har lokacin Momy tana zaune wucewa sukai suna tafiya 6angaren Mami humm tun daga harabar shashin suke jiwo tashin kid'a kallon juna sukai suna dariya domin ko ba'a fad'a ba sunsan Sultan ne shima yake nasa partyn suna shiga kuwa suka ganshi zaune ga mp a gefe sai kad'a kai yake ganinsu yasa Mami tai murmushi tana qare musu kallo tace. "Tofa 'yan matan Momy wato kuma Ashe kuna kan hanya inayiwa Sultan maganar ya rage qarar mp nan tayi yawa ku kuma wanka kuka d'auka kowa da kiwon daya kar'beshi kenan"? zama sukai Baby da har kamar tafi kowa jin farin ciki tace "Mami ba dole yau muyi tsalle mu jujjuya ba ya Ahmad ya fece ya bamu filin shan iska yau ranar gud'a ce muyi farin ciki muyi shewa yanzu ma mp Sultan muka zo mu ara zamuyi valentine a parlon Momy harda cake mukai saboda murnan ya tafi please Sultan bamu aro dan Allah" Baby ta fad'a tana mi'ka masa hannu bai kashe wa'kar da yake jiba ya mi'ko mata yana cewa. "Baza'a yi babu mu ba Aunty Baby ku tashi muje yau akwai buduri a gidan nan nima ina da chocolate gida guda bari in d'auko mu tafi da ita ku jirani" ya karasa maganar yana wucewa ya shiga bedroom d'insa kallonsu Mami tai tana cewa "yanzu ku da ace saikun fara ku ganshi ya dawo kamar a mafarki ya zakuyi"? Had'a ido sukai tare da jinjina kai a ransu suna hango irin hukuncin dazaiyi musu Baby tace "sai muce ba farin cikin tafiyarsa muke ba mu farin cikin yau wacce rana ma"? Ta tambaya tana kallon Khairat amsa ta bata "yau laraba". "Yauwa Mami kinga yau laraba sai muce murna muke taya Sultan tunda kinga ranar labara da dare aka haifeshi". "Ai kuma ba watan bane baku da yadda zaku kare kanku a gunsa" Mami ta fad'a daidai Sultan ya dawo yace "muje muyi partyn nan dan Allah ni harna fiku 'kaguwa" zasu fita Mami ta mi'ke tana cewa "bari nazo naga wanne irin shiri ku kaiwa tafiyar d'an nawa" ta fad'a ta biyo bayansu dariya sukai Khairat na cewa "gaskiya kam Mami ya kamata kizo ki gani kar ayi bake Momy kam dama tana gurin". "Nima ina biye daku yau zanyi kallo". Suna shiga suka ga prince Hamid a zaune ga Momy data kallesu taga harda Mami suka gayyato kawai tai dariya tana girgiza kai zama Mami tai tana kallon Momy tace "um muna can ashe suna nan suna shagali abinsu wai murnar tafiyar Ahmad suke"? Kai Momy ta d'aga tana cewa "eh haka suka ce gashi nan harda gayyatoku kuma mukam dama an dad'e da gayyarmu tun d'azu" murmushi Mami tai tana gyara zama tace "humn rabu dasu zanyi maganinsu" ta fad'a tana saita wayarta ta fara musu video duk abinda suke rufe baki Momy tai tana dariya Mami kam duk wani abu da suke tana d'auka Baby ce mai gabadatarwa kamar gaske Khairat ita da Sultan suna zaune kowa ya d'ora kafa d'aya kan d'aya idan tai magana sai su tafa mata harta gama Khairat ma ta kar'ba itama ta nuna murnarta da ranar 'yanci da suka samu sannan suka yanka cake duk abinda suke Mami tana tayi musu video Momy kuma datai sa'a Ahmad yana online tai kiransa video call duk abinda suke yana gani tsabar yadda suka bashi dariya har baisan lokacin daya saki murmushi ba gashi sun qure mp yaga harda prince Hamid dama yasan shine yake gayon bayansu kaiya jinjina yana katse kiran ya kira ta normal call yana cewa. "Momy kice ina magana dasu" kallonsu tai da murmushi akan fuskarta tace "Khairat da Baby ku kashe mp nan Ahmad zaiyi magana daku" Momy na fad'a d'iff Sultan ya kashe mp yana zaro ido yace "wanne Yayan"?. "Yayanku Ahmad gashi yana magana saiku karaso ku bashi amsa" ta fad'a tana mi'ka musu wayar rasa wanda zai kar'ba a cikin su akai domin sunji maganarsa da gudu sukai bedroom Sultan ma daya mi'ke da mpn sa a hannu ba arziki ya fece dariya sosai Mami tai tana cewa "ga tsoro ga rashin ji mukam munsha party sai ranar da Allah ya dawo dakai zasu sake yi mana irin wannan partyn na tayaka murnar dawowa gaskiya abun yayi dad'i sosai". Kai Ahmad ya jinjina yana cewa "zasu ci ubansu ne idan na dawo zasu san sunyi murnar nabar gida dani suke" yana rufe baki prince Hamid yace "to sarkin mugunta ba wani ubansu da zakaci kaima kasan dole suyi farin cikin barinka gida dan haka babu abinda zakai musu garama ka sani tun wuri" jin abinda prince Hamid yace yasa Ahmad yace "ai dama nasan kaine kake goyon bayansu kuma zasu gane ruwa ba sa'an kwando bane dani suke zancen kai kuma babu ruwanka tsakani na dasu ne ka gane"?. "Ban gane ba kasan Allah Ahmad baka isa ka yiwa yaran nan wani abu ba". "Haka kace"?. "Eh haka nace kuma babu yadda ka iya dani". "Ok ni kuma zan nuna maka isar tawa a aikace Allah ya dawo dani lafiya wallahi sai naci ubansu" yana fad'in haka ya katse kiran kallon Momy prince Hamid yai yana cewa "kiji fa Momy kiji abinda yake cewa ina ruwansa dasu yaran nan dole suyi komai idan baya nan shima ya sani saidai ya'ki Allah kawai mutum ya zama barazana ko motsinsa sukaji sai kiga suna shiga taitayinsu suna nutsuwa suyi shiru ko su nemi tashi subar gurin saboda dashi koda ace suna son zaman gun humm Allah ya dawo dashi d'in lafiya zan had'ashi da Abba yayi masa magana karya ta'ba lafiyarsu dan tunda yace haka saiya yi musu wani abu da hankalinsa ya kwanta ni kuma bazan bari ba" yana fad'in haka ya fita murmushi Momy tai tana cewa. "Zai huce kafin ya dawo yanxu ma ba fushi yayi ba kawai dai yace a basu wayar ne daga baya idan ya kira zanyi magana dashi" mi'kewa Mami tai itama tana cewa "bari na tafi Allah ya kyauta munzo munga party ai shi Sultan sarkin tsoro ya dad'e da guduwa". "Dole ya gudu kin manta shine mai mp sarkin DJ ya zama" dariya Mami tai tana cewa "uhm sarkin DJ manya zaici ubansa ai nasan idan Ahmad ya dawo sai yayi seizing d'inta". "Gaskiya kam tunda ya ganta kuma yaji kid'an shima Sultan d'in ba sha zaiyi ba ki huta lafiya". "Ok sai anjima" Momy ta fad'a daidai Mami ta fita itama Momyn ta mi'ke tana kallon kayayyakin da suka gudu suka bari kamar zatai dariya sai kuma ta girgiza kai tana wucewa. 🌆Russia🌆 Ahmad yana zaune bayan sun gama waya prince Hamid ya kirashi yayi masa tas akan su Baby dama ransa a 6ace yake baya so nan da gobe a samu wanda zaiyi masa magana cike yake dam da fushi ji yake kamar yayi fuffuka ya tashi ya koma gida yaci uban yaran nan ko zai sauka daga fushin da yake dasu yana cikin wannan yanayin Samir yazo ya sameshi baisan me yake faruwa ko meke damun Ahmad d'in ba kawai yana zama ya kalleshi yana cewa. "Yauwa Ahmad dama inata so na tambaye ka tun kwanan baya da dad'ewa lokacin danai kiranka wata budurwa ta d'aga baka nan tace min baka nan amma ita 'kanwarka ce dan Allah wacece ita ya sunanta"? Ahmad baiyi niyyar d'agowa ba saida yaji abinda yace ji yayi ransa ya sake 6aci fiye da d'azu da prince Hamid ya masa magana akansu Babyn tunda yaji yace 'kanwarsa yasan baby ce lokacin data d'aga harya fito ya sameta ya daketa da belt yanzu kuma shi Samir tambayar da yake a kanta me zaiyi mata............... "Ahmad baka fad'a min ba 'kanwarka ce"? A takaice yace masa "eh" cigaba Samir yai da cewa "wow masha Allah fad'uwa tazo daidai da zama mene sunanta sannan zan iya ganin photonta"? Wani kallon 'kasan ido Ahmad yayi masa ji yake kamar ya rufeshi da duka akan tambayar da yake masa amma saboda baya so ya fahimci wani abu sai kawai ya danne yace. "Sunanta Zuhra". "Wai Zuhra nice name daga ji kyakkyawa ce sosai zan iya ganin photonta"? Kai Ahmad ya girgiza da sauri ma kuwa yana cewa "a'a" da mamaki Samir yace "meyasa bakaza nuna min ba"?. "Saboda wani dalili". "Kai dan Allah Ahmad ka nuna min wallahi ina jin muryarta naji na kamu da sonta dama a 'kagare nake ka dawo na tambaye ka idan har zan samu ka shige min gaba na aureta wallahi da gaske nake maka Ahmad ina son 'kanwar nan taka fatan zaka bani ita................ Kusan numfashin Ahmad ne yaso ficewa yabar jikinsa tsabar yadda kalmar ina sonta da Samir ya fad'a ta daki zuciyarsa har saida ya runtse ido saboda jin wani abu kamar mashi ya soki zuciyarsa da sauri ya dafe 'kirji bai iya d'agowa ba duk da kiran sunansa da Samir yake saida aka dad'e kafin da'kyar cikin son danne 6acin ransa ya d'ago idonsa daya sauya kala muryarsa ma a sauye ba kamar yadda Samir ya sanshi ba yace. "Tana da miji". Zaro ido Samir yai yana cewa "dan Allah tana da miji Ahmad is this some kind of joke dan kaga yadda zanyi ne ka zolaye ni right"? Kai Ahmad ya girgiza yana cewa "Samir idan da zanyi maka wasa tun farko dana ja maka rai daka tambaye ni sunanta ina fad'a maka gaskiyar abinda baka sani bane a kanta domin anyi mata miji tana da wanda zata aura tunda dad'ewa lokaci ne bai karaso ba" Ahmad yai maganar da serious face musamman da yaga Samir d'in yana kokarin mayar da abinda ya fad'a masa wasa zazzafan huci Samir ya fitar yana kad'a kai yace. "Ok shikenan na fahimta amma banso wani yai min shigar sauri ba to amma Ahmad bayan ita baka da wata sister dan Allah nidai ina son nai aure a cikin 'kannanka muryar wannan ladyn taja hankalina sosai na shiga halin kamuwa da 'kaunarta please idan kana da wata 'kanwar bayan ita ina so dan Allah" a takaice Ahmad yace "Ina da ita amma itama tana da wanda zata aura". "Haba Ahmad bama haka dakai duk ta inda na 6allo saika zille ka sanni kasan halina sannan idan yaudara ce kasan bazan yaudari 'kanwarka ba dan Allah Ahmad ka taimaka idan kana da 'kanwa ka wacce take free ko Kuma wasa kake min please na had'aka da girman Allah ka fad'a min"? Ya fad'a harda had'e hannu ran Ahmad a dagule yace. "Bayan ita ba wata". Kai Samir ya girgiza yana shirin sake magana ganin bazai ha'kura ba yasa Ahmad yace "Samir kai aboki nane na ha'ki'ka kasan bana 6oye maka wani abu daya danganci sirri na amma nayi mamaki dana fad'a maka gaskiya ta yau ka kasa fahimta ta why"? Ganin da Samir yayi ran Ahmad ya 6aci sosai sannan yasan abinda ya fad'a masa gaskiya ne da ace 'kanwar tasa bata da miji bazai 6oye masa ba saboda akwai sha'kuwa da yarda mai 'karfi a tsakanin su tuna hakan yasa Samir yayi murmushi yana kallon Ahmad wanda ya gama cika yace. "Ok Ahmad kayi ha'kuri na 6ata maka rai ba a son raina bane nayi hakan ne saboda na nemawa kaina mafita". Kai Ahmad ya girgiza yana cewa "karka damu Samir baka 6ata min rai ba kafin 'karfin komai a guri na da ace ina da 'kanwa zan baka ita kaika san da haka". "Haka ne Ahmad ka fad'i gaskiya nagane ba damuwa Allah yasa gidajen zamansu ne". "Amin kawai shine abinda Ahmad yace daidai an kira wayar Samir ya mi'ke yana cewa "ok bari nazo Mum tana kirana". "Ok". Samir na barin gurin Ahmad ya d'aga waya ransa a 6ace ya kira numbern Khairat dan yasan idan ya kira Momy maybe basa kusa da ita Khairat suna zaune a bedroom jin wayarta na ringtone yasa da sauri ta d'aukota ganin wanda yake kira yasa ta tsaya cak tare da kallon Baby tana cewa "na shiga uku Baby shikenan na kad'e yau" da alamar tambaya Baby tace "meya faru waye ya kiraki" daidai kiran ya katse wani ya shigo a susuce Khairat tace. "Wallahi ya Ahmad ne yake kiran na" zaro ido Baby tai har ruwan data d'auka tasha ya 'kwareta ta kama tari da'kyar tace "ya Ahmad dai"? Kai Khairat ta d'aga tana cewa "ni yanzu bansan yadda zanyi ba kuma kar na'ki d'agawa na sake jawa kaina wani sabon laifin akan na d'azu". "To ki d'aga man tunda ba'a gida yake ba da sau'ki kome zaice tsakanin mu dashi da nisa bazai dake muba saidai fad'a da baki kawai" jin abinda Baby tace yasa Khairat ta jinjina kai a karo na uku da kiran ya shigo cikin azama ta d'aga tun kafin tai magana muryar Ahmad cikin tsawa yace. "Ummul-khairi uban me kikeyi baki daga min kira ba bayan kina gun raini ko"? Kamar yana ganinta da sauri ta girgiza kai tana cewa "dan Allah yaya kayi hakuri wayar tana bedroom tana caji ne mu kuma muna parlor saida muka shigo naga kana kirana kayi hakuri dan Allah" ta fad'a cikin son kare laifinta jin abinda da Khairat d'in tace yasa Ahmad sassauta murya yana cewa. "Okay ina Babyn take"?. Zaro ido baby tai tana rufe baki tare da yarfa hannu tana gwadawa Khairat tace bata gurin ita kuma bata fahimta ba saboda tsoron kar ta sake 'kular dashi tace "gata nan a kusa dani". "Bata wayar". Mi'ka mata Khairat tai da'kyar Baby ta kar'ba tsabar rawa da hannunta ya d'auka tana karawa a kunne tsawar da Ahmad ya daka yasa tai wulli ta wayar tana 'kan'kame jikinta kamar shine a gurin ganin da Khairat tai kiran bai katse ba yasa taje ta dau'ki wayar tana sake mi'ko mata a hankali saboda kar yaji cikin rad'a Khairat tace. "Baby kiyi magana kema kisan 'karyar da zaki masa ki fita kamar yadda nima nayi" Kai Baby ta girgiza zatai magana Ahmad yace "Khairat kina jina"? Da sauri Khairat tace "eh Yaya ina jinka". "Oh kina jina kuma dan ubanki nace ki baiwa Baby wayar kikai banza saboda kinsan bana ne ko"?. "Kayi hakuri Yaya gata nan kar'bi baby" ta fad'a tana mi'ka mata kar'ba Baby tai da yake hand free ne tana jinsa sosai yace. "Baby" Muryarta na rawa tace "na'am" jin ta amsa a fusace Ahmad yace "Baby! Baby!! Babby!!! na rantse da Allah duk ranar dana sake aje phone d'ina kika d'auka har kika sake yin magana da wani ban saka kiba saina 6allaki yau kin 6ata min rai sau biyu kenan ke kad'ai ki jira dawowa ta saikin shiga uku a hannuna had'uwar mu bazai miki kyau ba" yana fad'in haka yaja dogon tsuka yana kashe wayar d'ora hannu Baby tai akai tana kallon Khairat tace "na shiga uku Aunty Khairat me nayiwa ya Ahmad kuma ya taso da zancen tun d'aukar wayarsa da nai lokacin da abokinsa ya kira". Zama Khairat tai a bakin gado tana girgiza kai tace "to banace ba tunda kinga ya koma maybe abokin nasa ne daya kira kika d'aga yayi masa maganar ki kinsan dole ne zai tambayeshi wacece ta d'auka masa waya ko 'kanwarsa ce tunda yasan baida mata" jin abinda Khairat ta fad'a yasa Baby dafe kai tana cewa "innalillahi wa inna ilaihi raji'un Allah gani gareka kaine gatana ka fidda ni daga wannan damuwa data tunkaro ni". "Insha Allahu zai manta kafin ya dawo kar kisa abun a ranki harya dameki nasan yanzu ransa a mugun 'bace yake dan haka zuwa nan da kwana biyu zan kira miki shi ki bashi ha'kuri sannan ya huce" numfashi Baby ta sauke jiki a sanyaye tace "shikenan zan gwada Allah yasa ya kar'bi ban ha'kurin nawa". "Zai kar'ba kawai yanzu abinda zaki ki dage da addu'a kafin nan da kwana biyun wannan shine mafita" kai Baby ta d'aga tana cewa "bari na fara tun daga yanzu duk da ba'a makara wajen yin abinda ya dace bari nayo alwala" ta fad'a tana wucewa bathroom yayin da tabar Khairat itama tayi shiru ta shiga duniyar tunani............ ✍️MRS ÄL'ÄMËËÑ ÄHMÄD ÇË🌹. TYPING 📲Mon mar17/25 09:45PM YUSRAH 🤞 MUSA 🤞 ABUBAKAR 👑 ROYALTY 👑 💫A*W*A💫 Home of hospitality and harmony gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan ta haka taken mu yake tafiyar mu babu rago babu maci amana tsantsan gaskiya muke nunawa. _________________ __________________________ ___________________________________ ALLAH THE MOST HIGH DOESN'T SLEEP ALLAH THE MOST HIGH IS PURE HE ACCEPT ONLY WHAT IS PURE. Ubangiji ka sanya mana tsarkakar zuciya ya Allah kaine mai badawa ubangiji muna ro'konka lafiya a jinmu da ganinmu Allah ka bamu lafiya a duniyar mu da lahirar mu ubangiji ka kyautata makwancin mahaifan mu Amin. YÜSRÄH MÜSÄ ÄBÜBÄKÄR Wrïtër 1~ yarima Abdul-maleek 2~ Rayuwa biyu 3~ Safreeyyah 4~ D'an millionaire 5~ Dama kece 6~ Husnah ko Badiyat 7~ Minah-Umer 8~ Tajuddeen Aryam 9~ Me kamar sarki 10~ Minister Ashraf 11~ Yarima Aryan And now 12~ 👑Royalty👑 Later insha Allah👇 13~ 💘Zuciyar Aliyu ce💘 Yana nan tafe insha Allahu dana gama royalty zan fara shi akan #300 shima babu tsada sai dad'i. Littafai na basu da tsada sai dad'i da ilmantarwa da tunatarwa da kuma koyon darasi da hali masu kyau da d'abi'u na gari sannan ina saida su akan qaramin fara shi saboda masoya na duk mai bu'kata should DM me kayi min magana ta WhatsApp number na. +234 816 098 3083 Chat with me. Farashin book d'ina 01_Me kamar sarki #300 02_Safreeyyah #400 03~Minister Ashraf #300 Free kuma kyauta ne ga mai bu'kata shima should DM me. 01-Yarima abdul-maleek free book 02- D'an millionaire free book 03- Husnah ko Badiyat free book 04- Rayuwa biyu free book. 7~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Abidinah. @YUSRAHMS CE Page 13 & 14 Tunda Aiman ya tafi da Ayrah gidansu koda wasa bata sake le'ka su Hajiya Khubura ba tana gurin mahaifiyar Aiman tare da 'kannan sa har tayi 'kiba sakamakon d'an hutun data samu dama rashin kwanciyar hankali ne ya hanata sakuni duk kwanakin datai bata gidan Daddy bai ta'ba sani ba tsabar bata gabansa bai damu da ita ba har saida Hajiya Khubura ta gaji da aikin dasu Abidah suke yi saboda rashin Ayran ta samu Daddy ta fad'a masa 'karya da gaskiya sannan tace Aiman ya mayar da ita gidansu yace anan Daddyn bazai iya ri'keta ba bai damu da damuwarta ba kamar ba shine ya haifeta ba jin wannan maganar tai bala'in 6ata ran Daddy a take ya d'aga waya ya kira Aiman cewa yazo yana nemansa humm Hajiya Khubura abinda take so kenan dama ta samu Daddy ya kirashi tayi amfani da wannan damar tasa Daddy yasa Aiman ya dawo da Ayrah gidan ko yana so ko baya so, suna zaune a parlon Daddy ya shigo da sallama yana samun guri ya zauna cikin ladabi ya gaisa Daddy amsa masa yai yana kallonsa murya a nutse yace. "Aiman meyasa ka d'auke Ayrah daga gidan nan ka mayar da ita gidanku batare daka fad'a min ba"? Jin tambayar dayai masa yasa Aiman d'agowa ya kalli Hajiya Khubura wacce ta sakar masa murmushin mugunta tana jinjina kai alamar yasan aikinta ne kafin tai masa magana da ido tana kallon Daddy wanda shi kuma Aiman d'in yake kallo tace. "Ai dama na fad'a maka Alhaji bazai iya baka amsa ba saboda bashi da wata hujja haka kawai ya d'auke yarinyar yabar gidan da ita bayan baka gagara ri'ke iyalinka ba meka rageta dashi harda zaiyi abu batare da ya mayar dakai uba yayi shawara dakai ba" har lokacin idon Daddy yana kan Aiman yace "dashi nake magana kiyi shiru ke kam ina zuwa kanki" ta'be baki Hajiya Khubura tai tana juyar dakai gefe a ranta tace "ku gama ka dawo kaina d'in kome zakai wallahi sai yarinyar nan ta dawo gidan nan zan nuna maka kayi tsararo baka kaiba dani kake zancen ko Zainab bata isa ja dani ba balle wani banza kai data haifa". "Aiman". "Na'am Daddy". "Nace meyasa ka d'auke Ayrah daga gidan nan tsawon lokaci ban sani ba kuma kai baka sameni ka fad'a min ba" idon Aiman na kallon carpet yace "kayi hakuri Daddy nayi hakan ne bisa dole ba'a son raina bane saboda.......... Katse masa magana Hajiya Khubura tai da cewa "bada son ranka bane to waye ya saka ka dole ko Zainab d'in ce tace kazo ka d'auke ta"? D'agowa Aiman yai ya mata wani irin kallo batare daya bata amsa ba yaci gaba "Daddy maganar gaskiya Ayrah bata sakewa a gidan nan rayuwa take kamar tana gidan yari alhali ita da gidan mahaifinta bata da damar data isa zama koda na minti biyar ne a parlor kullum tana zaune guri d'aya daga bedroom sai bedroom sannan Hajiya tana gani 'ya'yanta Abidah da Nadiya suke dukanta su zageta su sakata wanki da wanke toilet gugar kayansu abincin su komai itace take musu sannan abun ba'kin cikin itace zatai komai ta kawo musu amma lomar abinci d'aya bazasu bari tayi ba a gidan nan saidai idan nine na shigo Mata dashi wannan dalilin yasa na d'auketa ta koma can suna zaune tare da Fati da Ashfat lafiya kalau kuma ta sake dasu sosai taji dad'in haka shiyasa nace bazata sake zaman cikin gidan nan ba saidai tazo musu da yawo shima idan kana nan" yana rufe baki Hajiya Khubura tace. "Karya kake munafiki wallahi Alhaji 'karya ya zauna ya shirya maka nice ina sane su Nadiya suke sakata wahala bayan su suke komai a gidan nan aiki kamar zai kashe su amma saboda baka tsoron Allah harda wani itace take mana komai tabd'ijan lallai ma yaron nan ba'a haifi abokin 'karya ka ba". "Ai dama ba dake nake magana ba da mahaifi na nake idan ke kin 'karya tani shi zai gaskata ni". "Shima bazai gaskata kan ba saboda babu gaskiya a cikin abinda ka fad'a sannan dole Ayrah ta dawo gidan ubanta harda wani ba dani kake magana ba da mahaifinka kake dad'in abun ma neman suna kake saidai kace ba dani kake magana ba da mahaifin wata ne ka gani domin a iya sani na 'ya d'aya ya haifa indai ba kalan dangi da son a sani ba ka daina kiransa da mahaifinka ka ri'ka cewa Yaya mahaifinka wannan shine "Bazance yayan mahaifin nawa ba Kinga Hajiya babu ruwanki anan zancen mune tsakani na dashi karki sake saka mana baki Ayrah kuma tunda ba kece kika haife taba dole ki d'auke idonki daga kanta idan kin 'ki akwai ranar nadama tana nan zuwa Ta'be baki Hajiya Khubura tai tana cewa "babu ranar da zata fito wacce a cikinta zanji nadama ta kamani rayuwa kuma yanzu na fara duniya yanzu nake jujjuya ta domin banyi komai ba ka zuba ido ka gani yanzu na fara tara tsinken dazan tsikari duniyar saina baka mamaki zaka yabawa aya za'kinta" Aiman zaiyi magana Daddy da abun ya ishe shi ya d'aga hannu yana cewa. "Ya isa haka ba hayaniya nake nema ba na tambayi Aiman ne inda Ayrah take kuma ya fad'a an wuce gurin tunda ka za'bi ta zauna a gidan ku shikenan hakan yayi zaka iya tafiya" a zabure Hajiya Khubura tace "zai iya tafiya zuwa ina? Gaskiya Alhaji bazata yuwu ba wai so kake a zageka a gari nima a zageni ace 'yarka d'aya ka kasa ri'kewa amma gashi ka ri'ke 'ya'yan ri'ko har mutum biyu". "Duk Wanda bai fasa cewa na kasa ri'ke 'yata na ri'ke d'an aro ba Allah ya tsine masa" Daddy ya fad'a a fusace. Ganin ransa ya 6aci yasa Hajiya Khubura take "A'a nidai Alhaji gaskiya kace ya dawo da ita gidansu ina tuna maka ne meka rasa me babu gidanka daci da sha bai kamata ace 'yarka ta tafi wani gidan can gayyar tsiya a karasa goyata ba dacan lokacin da mahaifiyarta ta rasu basu nuna zasu d'auketa ba sai yanzu data d'ago ta mallaki hankalinta sannan tsabar munafirci da yawan gulmar son a sani zasu wani ce zasu rike ta kace baka so ya dawo maka da ita yanzun nan ka tashi kaje ka dawo da ita". "Ai ba kece kika haife taba saiki bari wanda ya isa da ita yayi magana kuma indai umarnin kine bazan cika ba kin gane"? Kukan 'karya Hajiya Khubura ta saki tana cewa "yanzu tsakani da Allah Alhaji a gabanka yake cimin mutunci yana nuna ni uwar banza ce sai zagina yake yana mayar min da magana kana jinsa yana fad'a min abinda yaga dama? Wayyo Allah na ni Khubura shikenan yau na gamu da gamona" kai Aiman ya jinjina yana shirin magana Daddy yace "Aiman gobe idan Allah ya tashe mu cikin basu rai ina so ka dawo da Ayrah kamar yadda ka d'auketa" takaici ne ya kama Aiman musamman ganin irin kallon da Hajiya Khuburan take masa lokacin da Daddy yace haka kamar bazai tanka ba sai kuma yace. "Daddy ka bar Ayrah ta zauna acan bata jin dad'in nan gidan ko kad'an". "Haka tace maka bata jin dad'in zaman gidan nan ko kaine ka fad'a"?. "Bani na fad'a Daddy idona ne suka gane min". "A'a Aiman ka dawo da ita gobe da safe na gama magana tashi kaje" jin abinda Daddy yace yasa Aiman ya mi'ke ransa a 6ace ya fice daga parlon kamar jira Hajiya Khubura take yana fita ta sake matsawa kusa da Daddy tana kashe murya tace "nikam Alhaji ya maganar tafiyar Aiman makaranta ko ka fasa ne naji kayi shiru da zancen"? Kai Daddy ya girgiza yana cewa " a'a ba mantawa nai ba kuma ba fasawa nayi ba na gama komai lokacin tafiyar tasa ne baiyi ba saboda akwai wani mutum abokina ne da mukai magana tare dashi zasu tafi shi akwai abinda xanyi acan daya gama zai dawo Aiman kuma sai nan da shekara biyu idan ya kammala sannan zai dawo gida insha Allahu" Daddy na rufe baki Hajiya Khubura ta sauke wani daddad'an sansanyan numfashi tana sakin murmushin tsantsan farin ciki tare da jinjina a fili kuma sai tace. "To ikon Allah, Allah yasa ayi mai amfani nima dai Khaleel ya kirani a waya yau kusan kwana biyar yana fad'a min ya kusa dawowa gida kwanan nan" "kai Daddy ya d'aga yana cewa "ok Allah ya dawo dashi lafiya". "Amin Alhaji bari na duba su Abidah ko sun bar parlon nasan yanzu haka suna nan suna kallo ba hankali ne dasu ba idan na barsu zasu iya kaiwa asuba gara naje na korasu Ina dawowa" ta fad'a tana mi'kewa ta fita dama already tasan basa parlon kawai gulma ce take ciciyarta so take ta fad'a musu cewa Aiman zai bar gari ta huta dan bazata iya barci ba yau indai bata fad'a musu ba bedroom d'insu ta shiga suna zaune kowa da waya a hannunta tana chat tsaye Hajiya Khubura tai daga bakin kofar shiga bedroom d'in tana kallon su tace. "Albishirin ku kuce min goro" duk aje waya sukai suna kallonta tace "kuce goro idan ba haka ba bazan fad'a ba" d'an ta'be baki Nadiya tai tana mayar da hankalinta kan wayarta tace "dama dai Umma baki niyyar fad'a ba indai sai munce miki goro ne" ta fad'a tana sake gyara kwanciyarta Abidah ce kad'ai tace "albishirin mu goro manya farare tas 'kwalla 'kwalla masu girma fad'a mana meya faru na ganki cikin farin ciki haka Umma"? Murmushi Hajiya Khubura tai tana cewa. "Humm ba dole nayi farin ciki ba idan ta kama harda rawa zanyi yanzun nan nake magana da Alhaji sai na tambaye shi ya maganar tafiyar Aiman makaranta koya fasa yace a'a ya gama komai wai abokinsa yake jira su tafi tare fad'in haka shine ya saka ni murna annoba zai tafi ya barmu musha iska muyi abinda ranmu yake so batare da fargaba ba shiyasa daya d'auke Ayrah nasan yadda zanyi na zuga Alhaji yanxu yace lallai yana so gobe da safe ya dawo masa da ita" jin abinda ta fad'a yasa ba iya Abidah ba harda Nadiya wani tsalle sukai suna cewa "da gaske Umma"?. "Da gaske man saiku sake shiri kafin tsinanniyar ta dawo ni na koma kar Alhaji yaga na dad'e" tana fad'in haka ta fita kai Nadiya ta jinjina tana cewa "humm idan muka samu wannan takurar yabar gidan shikenan komai zai dawo mana sabo zamuyi abinda ranmu yake so babu fargabar komai tunda shima Daddyn ba zaman gida yake ba". "Uhm nikam bazan ce komai ba saita dawo bautar da zatai min bazai fad'u ba azaba zata sha iri iri wacce ta sani da wacce bata sani ba" Abidah ta fad'a tana d'aukar tata wayar itama taci gaba da chatting d'inta.......... Fitar Aiman gidansu ya nufa ransa a 6ace da yake ba sosai dare yayi ba yana shiga ganin babu kowa a parlor ya wuce part d'in mahaifinsa yana zaune ya shiga ganin yadda fuskarsa take yasa yace "Aiman lafiyarka kalau meya faru"? Zama zuciyarsa na 'kuna yace "Abba daga gurin Daddy nake yanzu akan na taho da Ayrah ran nan shine matarsa ta zugashi wai saita koma idan bahaka ba mutane zasu ri'ka masa kallon wanda ya kasa ri'ke 'yarsa ya ri'ke 'ya'yan ri'ko shine yace min dole saina mayar da ita gobe dan Allah Abba da safe kaje kace masa basai ta koma ba kaga ni 'kasar zan bari ga shegun yaranta bansan wanne hali zata tsinci kanta ba a gidan nan a haka ma suna ganin wulgina basu daina azabtar da ita ba balle akace sun tabbata bana gari abinda zasuyi mata bazai kyau banaso wani abu ya samu yarinyar nan" duk abinda Aiman ke mata Abba yana sauraron sa har yakai karshe kaiya jinjina yana cewa. "Shi Yayan ne yace ka mayar da ita gidansa daga nan kar ace ya kasa ri'keta? Kenan mu kasa ri'keka mukai shiyasa muka bar masa kai tun bakasan waye kaina harka taso har zuwa yau mun ta'ba cewa wani abu kodan ba laifin sabane mace ya aura gur6atacciya saidai muyi hakuri da komai amma ina mamakin yadda gabadaya ya canza rayuwarsa kamar wanda aka asirce? Allah ya rufa asiri karka damu Aiman zanje nayi magana dashi tashi kaje duk yadda za'ai Ayrah bazata koma can ba amma idan naga ya matsa lamba sosai zata koma tunda har ya nuna 'yarsa ce babu kara shikenan jeka" mi'kewa Aiman yai yana fita amma yasa a ransa Ayrah bazata koma gidan nan ba kome Daddy zaiyi tunda ba ra'ayin kansa bane sawar Hajiya Khubura ce zai nuna mata tayi kad'an. 👑 Palace 👑 Yau su Khairat basu wuni a sashin Momy ko Mami ba tun safe suka shiga fada gurin mai martaba Sultan Sharfaddeen tun safe har la'asar suna can sun saka su a gaba sai tsokana suke wannan yace wannan wancan yace wannan har saida mai martaba Sultan ya gaji ya kallesu yana cewa "kunga idan baku daina sakani magana haka ba zan kira muku Ahmad a waya na fad'a masa nace tunda ya tafi kullum sai kunzo kun dame ni" kallon juna sukai suna murmushi Baby data dau'ki wayarsa dake aje a kusa dashi tace "wow ya Ahmad zaka kira mana nikam waye ma Ahmad ne Aunty Khairat"? D'aga kai sama Khairat tai kamar gaske tace "bari na tuna nimafa ga dukkan alamu na manta shi kamar Ahmad sunan anguwa ko Sultan"? Ta fad'a tana kallon mai martaba Sultan tare da rufe baki ta soma dariya kai Sultan Sharfaddeen ya d'aga yana cewa "eh sunan anguwa ne anan tunda kun manta Ahmad amma baku manta Shadad ba ko shima bakusan shiba". "Eh to nidai kamar na san Shadad sunan wani lemo ne nima na ta'ba sha" Baby ta fad'a tana dariya "au da gaske sunan lemo ne"? "Kwarai sunan lemo ne yana can a wata qasa yana karatu". "To ikon Allah dama mutum ne kenan kuma kikace lemo ne"? Murmushi Baby tai tana d'aga kai tace "eh mutum ne saurayin wata nema shiyasa da akazo kansa batai magana ba tai shiru tana kallon mu" jin abinda baby tace yasa Khairat harararta tana cewa "dani kike kuma saina fad'a masa idan mukai waya". "Nima saina fad'awa nawa habibin idan kikasa ya dake ni shima yazo ya rama min". "Waye habibin naki"? Sultana Addah dake gefe ta fad'a tana kallon ta taji me zatace ko su Momy sun fad'a mata Ahmad na sonta ko kuma wani daban zatace............... Jitayi Babyn tace "habibina man wanda ban sanshi ba duk ranar da yazo saina fad'a masa nace inada yaya wanda ya dakeni ka rama min ko takawa ai nayi daidai ko"? Ta tambaya tana kallon Sultan Sharfaddeen kaiya d'aga mata yana cewa "eh kinyi daidai gara ya rama miki dama shima akwai zafin rai shikenan an had'u". "Waye me zafin rai"?. "Wani ne". "Bashi da suna" baby ta fad'a tana kallon sa "eh bashi da suna Zuhuriyyah ke kad'ai kin dameni wallahi tun safe kin takura min kuzo ku koma 6angarenku man". "Mufa mun dawo nan daga yau Allah yaja zamaninka da girma kujerarka takawa kakana Sultan Sharfaddeen" kallonta me martaba yai yana cewa "nikam Zuhuriyyah na tambaye ki man meyasa kike so kice min takawa" dariya baby tai tana kallon Khairat wacce itama ke dariyar tambayar da Sultan Sharfaddeen yai kafin ta mayar da hankalinta kansa tana cewa "ina nufin takawarka lafiya mai nasara Sultan Sharfaddeen mai martaba angon Sultan Addah Aisha masoyan asali haka nake nufi yanzu ka gane"? Kai ya jinjina yana cewa. "Na gane dama haka kike nufi"?. "Eh haka nake nufi kasan irinku sarakuna dole saida kirari da ace na iya da yanxu na rera maka amma yanzun ma idan kana son wa'ka nayi maka kana so"? Kaiya girgiza yana cewa "a'a bana son wa'ka wa'azi nake so idan kin iya kiyi min". "Na iya amma ni yanzu wa'ka nake so bari na rera maka kaida amaryarka Sultana Addariyah" "Kai harda 6ata mata suna"? "Ba 6atawa nayi ba kwaskwarima nayiwa sunan Aunty Khairat tashi mu tafi an kusa kiran magriba Sultan and Sultana ku huta lafiya" mi'kewa Khairat tai tana cewa "ki daina gyara musu sunan wai Sultan and Sultana tsofi ba ruwansu da wannan Sutalewar kawai kice tsoho Sharfaddeen da tsohuwa Addah". "To bazata ce hakan ba Sultan da Sultana zatace" Sultana Addah ta fada ganin Baby zata sake magana Sultan Sharfaddeen yace "dan Allah ku tafi mun gode da ziyara ku gaida iyayen naku" murmushi Baby tai tana cewa "to shikenan mun tafi ku huta lafiya Sultana Addah amaryar Sultan Sharfaddeen Aunty Khairat muje sai anjima" fita sukai mai martaba Sultan daya sauke numfashi yace "Allah ya shirye ku wadannan yara sam bakwa jin magana" yana rufe baki Baby ta le'ko tana cewa "ba tafiya mukai ba takawa muna tsaye dama jira muke muji me zakuce baku da wani abu da zaku bamu mun kawo muku ziyarar wuni guda mu tafi sungul kamar yadda muka zo"? "Eh babu abinda zamu baku yau sai kun sake dawo mana". "To shikenan amma idan zamu sake dawowa ku shirya mana liyafa kaji Sultan dan Allah"? "To za'a shirya muku sai kun sake dawowa muna jiranku". "Ko gobe ne mu dawo"?. "Eh Allah ya kaimu sai anjima ku tafi dan Allah kun dameni" dariya baby tai tana d'ago masa hannu tace "bye" juyawa sukai ita da Khairat suna fita motar da aka kawosu tana nan saidai da yake dama cewa drivern sukai ya tafi ya dawo ya d'auke su da la'asar ya dad'e da dawowar kawai zaman jira yake ganin sun fito ya tashi ya bud'e musu suka shiga ya mayar dasu saboda tafiya ce mai nisa tsakanin fadar Sultan Sharfaddeen da su kamar ba masarauta d'aya suke ba akwai tazara gidan yana da girma sosai. Momy tana zaune suka shiga ganinsu yasa tace "oh 'yan wuni sai yanxu kenan kuna can kuna takura musu ko"? Zama sukai baby na cewa "wallahi kamar kin sani muna can munata tsokanar su" "yayi kyau d'azu Ahmad ya kirani yana neman ku nace kuna gurin me martaba "ya Ahmad kuma yana neman mu meyasa bai kira a wayar Aunty Khairat ba"? "Ban sani ba kirashi ki tambaye shi kona kirashi na tambaya miki shi"? Zaro ido Baby tai tana cewa "ni a'a basai kin kira ba kawai dai nayi mamaki ne da kikace yana neman mu inaga yau ba fad'a zaiyi mana ba shiyasa bai kira wayar Aunty Khairat ba amma ranar ai kiranta yayi yasa ta bani wayar ya kashe min warning wallahi ranar da yana kusa nasan sai naci na jaki". "Me kikai masa ya kira yanai miki fad'a"?. "Uhm Momy idan ana sallah ba'a magana dama ya Ahmad a wuya yake dani yanzu kuma ki kirashi kice nace meyasa bai kira ta wayar aunty Khairat ba tab Allah ya rufa asiri ai inaga saiya dawo gida ya huce duk hushinsa a kaina". "Ai baki fad'a min me kikai masa ya kira yana kashe miki warning d'in ba"? Kallon Khairat Baby tai tana cewa "waifa Momy tun lokacin daya bar wayarsa a parlor ana kira na d'aga nace baya nan sai wanda ya kiransa yake tambayar wacece ni nace masa kanwar me wayarce shikenan daya fito ya kamani ya ri'ka min tsawa ya dakeni da belt bayana kusan fashewa yayi duk ya zama ja ban sani ba kuma wannan komawar tasa ko magana abokin nasa yayi masa a kaina shine ya taso da maganar ya kirani yace idan ya dawo na shiga uku nikam ina cikin tashin hankali". "Murmushi Momy tai tana kallon ta tace "babu abinda zaiyi miki idan ya dawo ki kwantar da hankalinki kafin lokacin dawowarsa yayi ya manta idan ma bai manta ba bazan bari ya ta'ba kiba" numfashi Baby sauke tana cewa "yauwa Momy nagode wallahi har naji dad'i da kikace haka" "uhm nikam dama ba ruwana dake kuka fi yi" Khairat ta fad'a tana mi'kewa ta shiga bedroom kallon Momy Baby tai tana cewa "to meyasa ni kuma nafi shiga tarkon ya Ahmad ne ko Sultan ma haka babu ruwansa sai lokacin da abu ya gifta amma nifa da nayi da kar nayi sunana zakiji yana ambata ko meyasa"? Murmushi Momy tai tana cewa "akwai abinda yasa yafi takura miki". "Meyasa Momy fad'a min ni kuwa insha Allahu daga yau zan kiyaye". "A'a baza'a ji mutuwar sarki a bakina ba ki bari idan Ähmäd d'in ya kira ki tambaye shi meyasa yafi matsa miki maybe ki samu amsa" jin abinda Momy tace yasa Baby ta zaro ido tana mi'kewa tace "ni na Isa na tambaye shi meyasa yake yawan takura min"?. "kin isa man ki gwada tambayarsa kiji"? "A'a Momy kawai abar maganar ya wuce bari nabi Aunty Khairat ciki naga me take kafin a kira sallah" ta fad'a tana wucewa da kallo Momy ta bita bayan ya bud'e kofa ta shiga tace "Baby bazaki san abinda yasa Ahmad yafi saka miki ido ba akan sauran saboda ya damu dake ne kuma yana sonki zaki fahimta zaki sani sai gaba amma ina tunanin ta yadda za'a fad'a miki wannan maganar ma ranar akwai damuwa da tashin hankali saidai zanyi kokari na ganar dake ta hanya mafi sau'ki yadda bazaki rigima ba" Momy ta karasa maganar tana sake kallon kofar shiga part d'in nasu kafin ta sauke ajiyar zuciya tana mi'kewa itama ta shiga nata part d'in......................... ✍️Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë 🌺. Be with me at always my lover's tnks for ur supports. TYPING 📲Tue Mar 18/25 11:11am YUSRAH 🤞 MUSA 🤞 ABUBAKAR 👑 ROYALTY 👑 ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫 home of hospitality and harmony gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan ta haka taken mu yake tafiyar mu babu rago babu maci amana tsantsan gaskiya muke nunawa. STORY WRITTEN ND EDITING Yusrah Musa Abubakar Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd Maman little Zarahn Aunty. 8~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Hamidinah. Bismilllahir Rahmanur Rahim 📿. @YUSRAHMS CE Page 15 & 16 Kamar yadda Hajiya Khubura ta fad'a ba'a dad'e ba Khaleel ya dawo kwanansa d'aya da dawowa yazo gurinta dayake Aiman baya nan baisan da zuwansa ba saida dare daya shigo gidan ya ganshi bai tanka ba ya share ya d'auka a take idan sun gama zancen zai tafi sai washe gari da safe ya ganshi har a dinning yana breakfast mamaki ne ya kamashi wato wannan 'kadagirin 'kato daga ina Kuma Hajiya Khubura ta gayyato shi humm kowacce bolar ta d'ebo saita kawowa mutane gida tsabar rainin hankali yanzu wannan shirgegen saurayin uban me ya biyota gidan aurenta yayi bayan 'yan matan da tazo dasu sannan shima ya dawo gunta da zama kamar wani 'karamin yaro humm zaiyi maganinsa kuwa domin kome Hajiya Khubura zatai sai Khaleel yabar gidan nan. Tunda Aiman yabar gida tun safe bai dawo ba sai bayan sallar la'asar yana shigowa da tasa motar Khaleel kuma ya fito daga gidan shima ya nufi tasa motar ya shiga yad'au wanka tsaki Aiman yaja ransa a 6ace da sauri ya karasa yai parking kafin ya fito har motar Khaleel taje bakin gate saboda dama me gadin bai mayar da gate d'in ya rufe ba tsaye Aiman yai yana bin motar da mugun kallo harya fice karasawa gurin me gadin yai yana cewa. "Daga yau karka qara bud'e masa kofa ko yanxu ya dawo kace na hana karya kuskura na qara ganin motarsa a gidan nan" yana fad'in haka ya juya da karfi ya shiga gidan zuciyarsa tazo wuya yana shiga Hajiya Khubura ta fito daga part d'inta ransa a 6ace yace "wannan gardin da kika kawowa mutane cikin gida kuma waye shi daga Ina"?. Wata uwar harara Hajiya Khubura ta sakar masa tana cewa "sannu d'an masu gida dad'in abun ma ba haka kawai ya shigo ba uwarsa ce ke aure a gidan kaga kuwa yana da 'yancin shigowa ko ba'ai masa izini ba kuma yana da gurin zama ko ba'a bashi ba". "Ok yana da gurin zama ko ba'a bashi ba kikace ko? To bismilllah yazo ya zauna d'in na rantse da Allah saina 6allashi idan na sake ganin 'kafarsa a cikin gidan nan saboda kina gadarar d'anki ne shine zai shigowa mutane gida kai tsaye haka da dagara yana wani hura hanci da bubbud'a kafad'u to bari kiji karya kuskura yace zaiyi mana hauka a gidan nan ina daidai dashi sannan karya kuskura ya ri'ka yin abinda zai sa6anta hankalina tsaf zanyi masa abinda zakiji ciwon sa domin niba shashasha bane irinsa bai isa yazo yace zaiyi abinda bai gamshe niba". Wani kallon sama da 'kasa Hajiya Khubura tai masa tana cewa "au sannu d'an me gida idan ya sake shigowa me zakai masa masa zaka dake shine"? Kai ya jinjina yana cewa "fad'a 6atawa idan kuma kina ganin nayi 'karya dan Allah ki kirashi yanxu kice ya dawo ya shigo gidan nan wallahi tallahi saidai a d'ebe shi zuwa asibiti" yana rufe baki Hajiya Khubura take "wallahi baka isa ka hanashi shigowa gidan nan ba saboda kaima ba gidan kune d'an karere ne dan haka kuwa baka da bakin cewa wani bazai shigo ba kaima alfarma akai maka". "Haka kikace"? A masife Hajiya Khubura tace "nace hakan kai abinda zakai". "Zakiga abinda zanyi d'in kuwa tsautsayi ya dawo dashi gidan yau zaiga hauka da d'anyan kai wallahi" ya fad'a yana shirin wucewa da sauri Hajiya Khubura tasha gabansa tana cewa "me zakai masa"?. "Bai shafe kiba nidai na fad'a miki sa'ko na zuwa gare shi ki sanar masa kar tsautsayi yasa naga wani abu sa6anin hankalina zaiga fushina akansa. "Wallahi baka isa ba dan gidan wan ubanka ne kace 'ya'ya na bazasu taka rawa da bazarsu ba dole su sakata su Wala a gidan nan tunda har Alhaji ya aure ni kai kuma babu yadda ka iya dasu sun zame maka ciwon ido idan ma ba'kin ciki kake da aureta da Alhaji saidai ka mutu babu yadda zakai ni dashi mutu ka raba" wucewa Aiman yai yana cewa "shikenan ni kuma zan gwada miki isar tawa Allah ya dawo dashi gidan zakiga yadda zanyi dashi" yana fad'in haka ya wuce da kallo Hajiya Khubura tabi bayansa harya fice tsaki taja tana cewa "jimin d'an mara mutunci to sainaga uban me zakai masa bari ya dawo gidan zansa yayi maka dukan halaka idan kaji wuya rainin da kake min zai ragu" ta karasa maganar tana wucewa domin yau dangin saurayin Nadiya zasu zo gidan kawo akwatun lefe Hajiya Khubura ta gayyaci manyan 'kawayenta suzo su kar'ba shine dalilin dayasa yau bata zauna ba tun safe take aiki har la'asar kuma abinda bata gane ba sannan bata damu ba da sukace sai dare zasu zo kawo kayan bata nemi dalili ba ita dai kawai su kawo. Bayan sallar magriba suka zo da kayan masu yawa kuwa wanda kowa mamaki take a cikin 'kawayen Hajiya Khubura wanne irin mutum Nadiya zata aura me kud'i haka Hajiya Khubura kam sai d'add'aga hanci take tana tausaya kai ta kalli nan ta kalli can har suka gama abinda zasuyi suka tafi zuwa bayan sallar isha da Daddy ya dawo sai sannan ta shiga part d'insa yana zaune ta sameshi itama zaman tai fuskarta fal da farin ciki dan harta manta warning d'in da Aiman yayi mata tana taso Daddy ya dawo ta fad'a masa saii kuma wadannan ba'kin suka zo shiyasa ta manta da wancan shafin kallonasa ta bakinta kamar zai yage ba sannu ba ya aiki da gajiya kawai abinda ke ranta take son fad'a kamar wani zai rigata tace. "Uhm Alhaji na manta ban fad'a maka ba d'azu dangin su Sabit sunzo baka nan naso kiranka amma kuma hidima ta hana saidai Kai fatan alkhairi" da alamar tambaya Daddy yace "su waye kuma dangin Sabit"?. "Saurayin Nadiya fa nake magana akai d'azun daf da zaka dawo suka tafi". "Ok aure zaki mata"?. "Eh har an gama komai ma rana tayi nisa d'an lokaci ya rage" kai Daddy ya jinjina yana cewa "amma baki ta'ba fad'a min ba kunyi bincike a kansa ne d'an waye shi"? Kai Hajiya Khubura ta girgiza tana cewa "ai Alhaji sun dad'e ba wani bincike da za'ai tunda kusan shekaru hud'u baya da suka wuce yana sonta". "Ba maganar dad'ewar da sukai nake ba magana nake akan kunyi bincike a kansa ne"?. "A'a bamuyi ba". "To meyasa"?. "Alhaji gani nayi Nadiya tasan yaron nan sani na ha'ki'ka nima na sanshi yawancin lokuta tana kawo min shi ya gaishe ni gaskiya yana da nutsuwa bashi da gurin kushe ko kad'an nasan zai ri'keta da kima sosai" kai Daddy ya sake girgizawa yana cewa "wannan fa duk ba hujja bace Khubura maganar sun dad'e suna soyayya kema kin sanshi duk bazai gamsar ba abinda ya kamata shine kuyi bincike kafin ku fara komai wannan shine ya asalinsa yake ya mu'amalarsa da iyayensa take bawai kawai kice min kin sanshi yawancin lokuta yana zuwa gaisar dake ba gaisuwa da lokaci kad'an dazai tashi ya tafi taya zakisan halinsa yaron kirki ne ko na banza sannan idan ya aureta zai ri'ke miki ita ke duk bakya tunanin wannan"? Tunda ya fara magana Hajiya Khubura take faman murgina kai ta juya nan ta juya can ta ta'be baki alamar maganganun sa basu samu kar6uwa ba jin yayi shiru ta d'ora nata. "Alhaji naji duk abubuwan daka fad'a wannan gaskiya ne haka yake saidai kar kace ban bi shawararka ba ko ban dau'ki abinda ka fad'a min da muhimmanci ba a'a na yarda da dukkan komai abinda kace amma fa ni na riga na yanke hukunci koma waye shi sai Nadiya ta aureshi saboda da alama ba d'an 'kananun mutane bane iyayensa suna da 'kazamin kud'i idan na samu Nadiya ta aureshi bani ko jikanu naba hatta tatta6a kunne na sai sun taso sunci irin dukiyar kaga kuwa ina zan sake ya kubce mana abu nefa ake nema sai gashi yaso har gida kasan ko bazan sake ba dole nema Nadiya ta auri Sabit ko bataso balle itama masifar sonsa take kamar ranta" tunda Hajiya Khubura ta fara magana Daddy ke girgiza kai cikin yanayin rashin jin dad'in son zuciyar data nuna 'kiri-'kiri har takai aya kafin ya kalleta dakyau yaga bil hakki tsakanin ta da Allah tayi maganar ta kuma babu batun komawa da baya ko ace wannan maganar auren ta wargaje a 6angarenta. "Khubura" taji Daddy ya kira sunanta amsawa tai tana 'kureshi da kallo domin taga sauyin yanayi a fuskarsa da alama dai neman hanata samun wannan d'aukakar data sameta yake shirin yi jin a karo na biyu ya sake cewa. "Khubura" bata amsa ba sai caraf datai tana cewa "Alhaji wai me kake nufi ne amma ba hana auren nan ne niyyarka ba gaskiya nikam ina so kuma yarinya ma tana so dan haka babu wata magana kawai ka bimu da fatan alkhairi a gani na zaifi" ta karasa maganar harda irin d'aga kafad'ar nan. Ganin ta riga tayi nisan da baza taji kira ba Daddy yace "Ok ai shikenan Allah ya sanya alkhairi Allah yasa gidan zamanta ne Allah ya bada sa'a" kawai shine abinda yace daga haka yai shiru saidai abun nacin ransa kamar 'yarsa ta cikinsa Hajiya Khubura take shirin yiwa haka amma tunda ta nuna 'yarta ce shi bai isa ya fad'i magana a kanta ta d'auka ba zai zuba mata kamar yadda ta bu'kata a yayin da wata matsala ta shigo ciki shima lokacin zai nuna mata Nadiya ba 'yarsa bace 'yarta ce babu ruwansa a ciki......................... Ganin yayi shiru yasa Hajiya Khubura ta kalleshi tana cewa "Alhaji dama ina so na fad'a maka Khaleel ma yaga Ayrah ranar da tazo gidan nan d'iban kayan sawarta yace yana sonta na fad'a maka idan zaka bashi aurenta"?. Numfashi Daddy ya fitar yana cewa "mezai hana indai Allah ya 'kaddara matarsa ce shikenan bani daja Allah ya za'ba mana mafi alkairi a rayuwar mu" yana rufe baki Hajiya Khubura ta saki wani irin murmushin jin dad'i ganin shima ya amince shikenan kwanan nan zata zama Hajiya Khubura billionaire mai nairori tayi suna a yankin Africa da yankin yirof ko ina a santa ayi da ita ta kafa kamfaninnika ta zuba ma'aikata yau tana wannan kasar gobe tana wancan wannan shine burinta iya tunanin hakan datai ya sanya mata wani jin dad'i da sanyi yana shiga zuciyarta mi'kewa tai cikin 'kwarin gwiwa tana cewa. "Yauwa Alhaji muna godiya da wannan karamcin naka bari naje na fad'a masa wannan daddad'an albishir d'in" ta fad'a tana ficewa da sauri kamar zata kifa ta shiga wani part data baiwa Khaleel matsayin ya dawo gidan da zama saboda ta had'a Aiman da Daddy ya hanashi yace ya 'kyale kar yayiwa Khaleel magana shiyasa yanzu Aiman baya shigowa gidan ko kad'an sun daina ganinsa tunda dama Ayrah bata nan tana gidansu yanzu shi damuwarsa lokacin tafiyarsa Beijing yayi kawai yabar Nigeria ya huta da kallon kayan ba'kin ciki da takaici. Khaleel yana zaune a parlor ya 'kure sauti kamar ba dare ba kana ganinsa kasan sai a hankali d'an sharholiya ne hutu kawai ya sani bayan haka baisan komai ba saidai yaci yabi lafiyar gado yana wannan halin Hajiya Khubura ta shiga ganinsa zaune yana kad'a kai alamar sautin kid'an yana tsuma shi ga wani arnen d'an mitsilin wando a jikinsa mai kamar da d'an diras cinyoyinsa sad'a-sad'a a waje maimakon ace tayi masa fad'a sai murmushin ya burgeta d'anta wayayye ne data saki tana zama ta kalleshi idonsa a rufe da 'karfi tace. "Khaleel" bai bud'e idon nasa ba balle yasan tanayi saida ta sake 'kwalla masa kira tana d'an ta'ba kafarsa sannan ya bud'e ido yana tashi zaune daga jinginen da yake ya kalleta yana cewa "Umma yaushe kika shigo kin sameni ina shan DJ" murmushi tai tana d'add'aga hanci ala dole ita mai d'a tace "dama zuwa nayi muyi magana Khaleel ko Alhaji zai kiraka na akan maganar kana son Ayrah ka tsaya ka nuna masa sosai kake sonta saboda Naga shi haka shine damuwarsa na riga na fad'a masa cewa kana sonta zaka aureta" da mamaki Khaleel yace "amma meyasa Umma nifa bana jin son yarinyar nan a raina meyasa kika ce masa haka"? Gyara zama Hajiya Khubura tai tana cewa "kasan dalili kaga niba haihuwa nayi da Alhaji ba ga 'kazamin kud'i daya tara kamar qasa kasan idan ya mutu iya tumuni zan samu gabadaya dukiyar ta Ayrah ce amma abun hikimar anan shine idan akace ka aureta ta zama matarka saiya mutu to kaga komai yana hannun mu dukiyar ma ta zama tamu karshe saimu samu mu kashe Ayran batare da sanin kowa ba mu mallake komai kasan wannan shawarar tawa tayi sabida kaima kana son ka inganta rayuwarka ko amma me kace"? Shiru yayi zuwa wani lokaci ya d'ago yana jinjina yace. "Tabbas Umma wannan shawara taki tayi kwarai zan aureta ko yanzun nan ne na shirya ki sameshi ki sake fad'a masa sannan ki nuna kawai nine na ganta nace ina sonta ba kece kika fad'a ba sannan maganar daga ni take" ajiyar zuciya Hajiya Khubura ta sauke tana cewa "yauwa Khaleel ko kaifa har kasa naji dad'i wallahi bari na koma kar Alhaji yaga na barsa shi kad'ai" ta fad'a tana mi'kewa ta fita da kallo khaleel yabita harta fita daga baya ya sauke ajiyar zuciya yana sakin murmushi tare da mi'kewa ta tafi jikin window ya d'aga labule yana kallon waje a ransa yana cewa. "Gaskiya Umma kin iya had'a shiri ban ta'ba kawowa a raina zan kalli wannan yarinyar ba saboda yayan nan nata Aiman masifaffe ne amma yanzu tunda har Daddyn ta ya shiga ciki na sake samun 'kwarai gwiwa ta yadda zan tareta da karfina duk sanda nake so" kaiya jinjina yana cije lips ya murza yatsunsa suka bada sautin 'kas 'kas kafin ya cika bakinsa da iska yana firzarwa a fili yace "muje zuwa shiri nagaba na kusa taka wani matsayi da nake son zuwa" bai baro jikin windown ba yaci gaba da tsaiwa a gurin kawai yana kallon waje iska tana shigarsa yana lumshe ido yana bud'ewa cikin yanayin da rabon daya jinsa a irinsa harya manta sai yau da yaga ya samu dami a kale Hajiya Khubura tai masa hanyar samun cikakkiyar budurwa yana zaune batare daya sha wahalar komai ba. ***Bayan sati biyu Aiman ya gama komai nasa lokacin tafiyarsa Beijing yayi saidai a yau d'in dazai tafi sai yaji wani 6angare na zuciyarsa yana riya masa baya so ya tafi yabar Ayrah baisan wanne hali zata shiga ba Allah yasa bayan tafiyarsa kar Hajiya Khubura ta zuga Daddy yasa Ayrah ta koma can itama Ayran a nata 6angaren duk hankalin ta ya tashi tasan idan har Aiman yabar gari zai wuya Daddy baisa ta koma can gidansu ba ita kuma hakan ne bata so musamman ranar da taje d'iban kayanta taga khaleel a parlor ga wani irin shu'umin kallo da yake binta dashi yana d'age mata gira yana lashe baki tun da taga haka tsoro ya kamata bata sake zuwa gidan ba har yau shiyasa take tunanin tafiyar Aiman d'in har wata ramar rashin kwanciyar hankali tai gashi a hakan ma tana gidan hutu ne babu me takura mata da ace a gidansu take maybe da yanzu ta kamu da ciwon bugun zuciya. Duk suna zaune a parlor suna jiran fitowar Aiman suyi sallama kowa ka kalla fuskarsa fal dake da damuwa shi kanshi Aiman baisan wannan tafiyar yanzu zaiso ace a qara masa lokaci zuwa gaba amma dai kawai ya danne duk yadda yake ji bayan ya gama shiryawa ya goyo jakarsa a baya hannunsa kuma ri'ke da trolley yana ja ya fito ganinsu zaune fitowarsa duk sun zuba masa ido yasa ya d'an dakata yana sauke numfashi kafin ya karaso yana zama ya kalli mahaifiyar sa murya a nutse yace. "Aunty Umma lokaci yayi zan tafi ina so kimin addu'a sannan magana ta karshe dan Allah duk yadda zaki karki bari Ayrah tabar gidan nan karta koma gidansu komawarta can akwai had'ari barazana ce ga rayuwarta wadannan yaran suna matsa mata baya da haka yanzu wani saurayi yazo gidan wai shima d'anta ne harda part aka bashi a gidan ya d'auko kayan sawarsa da motarsa da komai nasa ya dawo gidan kuma Daddy ya sani amma bai hana ba shiyasa ni nake fargabar barina gari domin indai Hajiya Khubura taji labarin tafiya ta saita zuga Daddy yasa Ayrah ta koma dan Allah Aunty Umma karki bari ta koma" ya karasa maganar yana kallon Ayrah wacce zafafan hawaye suka zubo mata shiru yayi zuwa wani lokaci ya sake d'agowa yana cewa. "Ayrah kiyi hakuri komai ya zafi maganinsa Allah ki daina kukan nan haka insha Allahu nasara tana tare dake babu wanda zai samu d'aukaka saiya sha wahala sannan ba'kin ciki yana tare da farin ciki tsanani yana tare da sau'ki ki ri'ke wannan a ranki kullum ki kasance mai godiya ga Allah domin wannan yanayin da kike cike hakan ma baiwa ce karki fushi ki zama mai godewa Allah a kowanne hali ubangiji maji ro'ko ne idan kika tsaya a kofarsa zai kar'be ki idan kika nufesa zai cika miki burinki karki sare karki nuna karaya wata rana wannan kukan da kike zai zama miki dariya mai d'orewa ki dauwama a cikin farin ciki gaba kinji" jiki a sanyaye Ayrah ta d'aga kai tana shasshe'kar kuka ta kasa magana sosai ran Aiman ya dagule amma bashi da yadda zaiyi yana fatan tafiyarsa ce mafi alkairi akan zamansa sannan yana fatan Ayrah a duk inda ta tsinci kanta ubangiji ya zame mata kariya da garkuwa. Mi'kewa yai bayan Aunty Umma ta gama yi masa addu'a da fatan samun nasara karatun da yaje nema ya samu Allah ya dawo dashi lafiya shigowa Abba yai yana kallonsu da yanayin fuskokinsu kafin ya mayar da hankalinsa kan Aiman da shima fuskarsa a 6ace take yace. "Lokaci yayi Aiman ka gama sallama da Umman taka da 'yan uwan naka ne"? A hankali Aiman ya d'aga kai tare da mi'kewa bai sake kallon inda Ayrah take ba muryarsa da rauni yace "na tafi" bai jira amsar kowa ba yayi waje Abba yabi bayansa hannu Ayrah ta d'ora aka tana fashewa da kuka a susuce ta mi'ke zata fita itama ko mayafi babu a jikinta balle takalmi da sauri Aunty Umma ta ri'keta tana girgiza mata kai babu bakin magana domin idan har tace zatai magana tofa kuka ne sakamakon dazai biyo baya kawai jawo Ayrah jikinta tai dan ta samu nutsuwa ta fara shafa bayanta a kunnensu sukaji tashin motar Abba da zai kai Aiman airport inda abokinsa yake yana jiran zuwan su. Kwana biyu da tafiyar Aiman Hajiya Khubura ta hura wutar dole sai Daddy yasa Ayrah ta dawo gidansa yasa ta baro gidansu Aiman farko Daddy ya share tun yana baiwa iska ajiyarta harta isheshi da 'korafi kullum bata da aiki sai yi masa mita gabadaya tabi ta d'aga masa hankali ta had'a masa zafi sam yanxu baya jin dad'in zaman gidan idan ya dawo daga aiki ko bari ya huta bazatai ba zata fara yi masa maganar Ayrah shi kuma a nasa 6angaren Ayrah bata cikin rayuwarsa bai damu da duk inda ta shiga ba amma saboda hanashi sakat d'in da Hajiya Khuburan take yasa da kansa yaje ya sami Abban su Aiman ya fad'a masa yana son Ayrah ta tattara kayanta ta koma gidansa tunda Abba da Aunty Umma sukaji wannan maganar sun san had'in Hajiya Khubura ne amma babu wanda ya tanka a cikinsu domin basu da iko akan Ayran tunda mahaifin ta nada rai kuma ya bu'kaci kayarsa ta koma garesa fatan su Allah ya tsareta a duk inda take nasiha sosai suka had'u sukai Mata cewa tayi ha'kuri da duk abinda ta zata gani idan ta koma Kuma ta ri'ka hattara da taka tsantsan sabida sun samu labarin d'an gidan Hajiya Khubura ya dawo gidan da zama suna jin tsoron karya 6ata mata rayuwa amma gudun abinda zaije ya dawo kawai sukai ha'kuri ba a son ransu ba Ayrah ta tattara kayanta tana kuka sosai a dolen dole ta koma gidan humm tun daga ranar tasan ta koma azaba sabon takura da azabtarwa iri iri ta fara fuskanta musamman yanzu da suka san Aiman baya Nigeria gabadaya yayi nisan da ko kasheta zasuyi su binne baida damar iya cetonta............................. ✍️Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë 🌺. We will meet again. Ina godiya masoya godiya sosai sosai godiya Allah ya sake barinmu tare. See you tomorrow morning. Be with me at always my lover's. TYPING 📲 +234 816 098 30 83 YUSRAH MUSA ABUBAKAR ✨✨. 👑 ROYALTY 👑 ______________ _______________________ _________________________________ 💫A*W*A💫 Home of hospitality and harmony gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan ta haka taken mu yake tafiyar mu babu rago babu maci amana tsantsan gaskiya muke nunawa. Naja'at Musa Abubakar Abubakar Musa Abubakar. Wannan page d'in naku ne kyauta kuyi yadda kuke so dashi. 9~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Salihinah. Bismilllahir Rahmanur Rahim 📿. @YUSRAHMS CE Page 17 & 1️⃣8️⃣ Tun kafin kiran sallar asuba wajen karfe biyu da Ayrah ta farka bata sake iya komawa barci ba tsabar damuwa datai mata yawa tana kwance shiru idonta na tsaye tana kallon p.o.p d'in d'akin gajiya tai ta tashi zaune tana tagumi kawai tunanin yadda gobe zatai dasu Abidah take yi tunda ta dawo kiran sallar asuba na farko basa barinta ta sake da'kyar zasu d'aga mata qafa tai sallah daga nan idan suka sakata gaba da aiki da zagi da tsangwama sai idan Kiran sallar azhar akai dasu barta taje wani gun shima tanayin sallah zata dawo musu kuma a hakan daidai da lomar abinci d'aya basa bari tayi saidai idan ta faki idonsu ta d'iba ko a kitchen d'in agurguje taci dan karsu ganta ta rasa me tayi musu a rayuwa wannan tsanar da suke mata har ina bataga abinda ta tare musu ba itace ya kamata tayi musu ido idanma batun rashin mutunci ake tunda dai sune suke zaune a gidan mahaifin ta matsayin agololi amma sai abun ya juye kanta tana 'yar gidan amma ko 'yar aiki bazata fad'a mata bautuwa da shan wahala ba zataso ace ta samu wanda zata karantawa damuwarta wanda zai funkance ta ya gane tana tsaka me wuya ya ceceta tana so hankalin mahaifinta ya dawo kanta ya nuna mata gata da kulawa kamar yadda yake mata da meya sameshi ne meke damunsa wa zata samu taiwa wannan tambayar a ina zata samu amsa wa zata karantawa matsalarta yanzu wa take dashi babu kowa babu me damuwa da damuwarta yanzu kukanta banza babu me share mata gashi Aiman yayi mata mugun nisan da kafin ya dawo su had'u idan kasheta zasuyi sun kasheta Daddy babu ruwansa ko a gabansa zasu zageta su daketa bazai tanka ba bazai nuna yaji zafi ba saboda bata cikin zuciyarshi an riga da an raba soyayyar da yake mata daya zata dawo da tunanin mahaifin ta daidai wannan shine mafita da hanya ta farko da zatabi wajen gyara matsalar cikin gidan ta sani muddin akace Daddy ya dawo hayyacinsa tofa itama ta warke sannan gaskiya zatai halinta Hajiya Khubura da 'ya'yanta lokacin nadamarsu da shiga ukunsu yazo to amma taya zatai hakan wa zata samu ya taimake ta? "Babu kowa" itace amsar domin babu wanda zata karantawa tun ranar da Hajiya Khubura ta matsawa Daddy sai yaje ya taho da Ayrah daga gidansu Aiman bayan yaje ya sakota a gaba sun dawo gidan a gaban Hajiya Khubura yayi mata tas yace kuma bai amince ta sake koda kallon gidansu Aiman ba balle ta shiga duk ranar data sake zuwa gidan yaji labari saiya dau'ki mummunan mataki a kanta yayi mata iyaka dasu har abada ga 'karamar wayar da Aiman ya sai Mata saboda su rika magana Hajiya Khubura ta kar'be tun ranar data ganta a hannunta sau d'aya tai waya dashi tasan yana can cikin rashin kwanciyar hankali tunda baisan wanne hali take yanzu ba, ba lallai ya iya karatu yadda ya kamata ba ko tanan sun shiga hakkinsa indai bai tsaya yayi abinda ya kaishi ba tuna hakan datai yasa batasan lokacin data fashe da kuka tana kifa kanta akan cinyarta ba kuka take sosai babu me cewa tai shiru ko me yake damunta harta shafe lokaci tana yi ta ha'kura ta koma sauke ajiyar zuciya karshe ta mi'ke jiki a mace kamar mara lafiya ta nufi toilet tayo alwala tazo ta fara nafilah tana ro'kon Allah ya kawo mata canji a rayuwarta ya kawo lokacin da hankalin Daddyn ta zai dawo jikinsa har lokacin sallah asuba yayi tana kan sallaya tana addu'o'i jin an shiga sallah itama ta mi'ke tabi jam'i ana sallama ta aje hijab d'inta da sauri ta saka takalmi ta fita zuwa main parlor ta soma goge-goge kamar yadda suka umarce ta basai sun tuna mata ba saboda sunce tunin da zasuyi mata d'an banzan duka ne shiyasa take taka tsantsan tunda yanxu babu me cetonta ko zasu sakata a inji su markad'a. Saida ta gama danan sannan ta wuce kitchen ta d'ora musu abincin breakfast saboda yanzu time table suka kafe mata a jikin kofar kitchen d'in kowacce rana da abinda zata girka musu harta gama komai takai dinning babu wanda ya fito kuma a 'ka'ida bata Isa ta koma bedroom d'inta ba sai sun fito ta shiga part d'insu ta gyara musu ta had'a musu ruwan wanka sannan ta shiga part d'in Hajiya Khubura ma yanxu kuwa har part d'in khaleel itace take sharowa ko inji bazai fad'a mata aiki ba................... Tana zaune a qasan carpet jin an bud'o kofa yasa da sauri ta kalli gurin Daddy ne ya shigo da alama daga masallaci ya dawo bayansa kuma khaleel shima yasha jallabiya kamar mutumin kirki ganin Daddy yasa Ayrah ta sake dur'kusawa sosai tana cewa "Daddy ina kwana"? Shiru yai zai wuce bai amsa ba ta d'auka baiji bane saita sake cewa "Daddy ina kwana"? Tsaki yaja wanda saida tajisa kafin can qasa yace "lafiya" yana fad'in haka ya bud'e kofar part d'insa ya shige da sauri saboda baya son ganinta kawai dan babu yadda zaiyi ne dole Hajiya Khubura tasa ya dawo da ita daga gidan su Aiman amma shi zamanta acan ma yafi masa dan dai ba yadda zaiyi ne. Tsaye khaleel yai a kanta yana qare mata kallo kanta na qasa amma hankalin ta yana kansa domin tasan maybe tunda taga ya tsaya akwai abinda zaice ta tsani gayen nan bata kaunar ganinsa.............. A firgice ta zabura tana mi'kewa tsaye jin ya dafa mata kafad'a ganin yadda ta susuce yasa ya kalleta yana murmushi tare da d'age gira yace "yadai Baby me kike haka kamar ba wayayya ba daga na d'an ta'ba ki saiki wani zabura haka meyasa bayan kinsan ni ba wani abu zanyi miki ba look madam muje part d'ina ina so muyi magana dake kinji"? Da sauri Ayrah ta girgiza kai idonta na cika da hawaye ta soma jada baya kaiya jinjina ganin tana shirin zubawa da gudu yai caraf ya ri'ko hannunta ihu ta sakar masa da sauri ya sake mata hannu yana jan tsaki kawai ya zafga mata harara yana cewa "banza mara 'kwa'kwalwa 'yar 'kauye kawai nine zan ta'ba ki kisaka min qara saboda baki da hankali? Humm zan kamaki ne zaki bayani badai nine meke ba akwai ranar da zaki tsinci kanki a hannuna cikin bedroom d'ina akan gadona🙊 sai yadda naga dama nayi dake kuma zaki gani" yana fad'in haka ya wuce jin abinda yake fad'a yasa Ayrah ta fashe da kuka da gudu ta shige part d'inta hankalinta a tashe me yake nufi da shine me ita sai yadda yaga dama da ita badai aurenta zaiyi ba Allah yasa ba haka yake nufi ba indai kuwa ya kasance hakan nr gara mutuwarta data yarda wannan khaleel d'in d'an gidan Hajiya Khubura ya aureta ina zata samu damar magana da Yaya Aiman ta fad'a masa abinda yake faruwa kar suyi mata auren dole dashi innalillahi wa inna ilaihi raji'un kawai shine abinda take iya maimaitawa numfashinta na sama-sama kamar wacce tai gudu tashi tai ta rufe kofar bedroom d'inta saboda tsoron kar wani ya shigo mata a cikin su Abidah tasa a ranta yau ko kasheta zasuyi bazata fita ba saidai su 6alla kofar su shigo, kwanciya tai tasa bargo ta lullu'be jikinta kamar me barci a zahiri kuwa idonta biyu kawai shiru tai ta zurfafa cikin tunani yau ta ha'kura ko school bazata jeba. Su Abidah duk basu san abinda ya faru tsakanin Ayrah da khaleel ba saida suka fito yin breakfast sukaga batazo serving d'insu ba tsaki Nadiya tai tana kallon kofar part din da Ayran take tana cewa "wannan munafikar yarinyar ubanta take a part d'in nata ne da bazata fito tayi serving d'in muba aiko wallahi ta sake naje kiranta sai nayi mata mitsiyacin duka kafin na jawo 'kafarta a 'kasa na kawota nan na sake cin uwar ubanta haba dan rainin hankali kullum yarinya sake zama jaka jahila take". "Jeki fito mana da ita dan kan uwarta" Hajiya Khubura ta fad'a tana hararar kofar part din itama mi'kewa Nadiya tai a fusace tana cewa "wallahi ta bari naje kiranta saita gane Allah da girma yake" ta fad'a tana wucewa itama Abidah mi'kewa tai tana bin bayanta tace "muje tare nima fushina yazo wuya saboda yau da yunwa na tashi ita kuma 'yar bankad'add'un ta sharemu" Nadiya tana kokarin bud'e kofa tace "yau zataga yadda ake shariya ganin idonta dan idan na fara guzarta sai naga jini yana fita a jikinta dama Aiman nake tsoro kuma baya nan uwar ubanta yau xata ci" shiga sukai amma kofarta a kulle 'kam kwankwasawa sukai shiru babu koda motsi bugawa suke kamar zasu karya kofar Ayrah na jinsu tai banza ko motsawa daga kwancen da take batai ba gajiya sukai da kwankwasawa suka tsaya kowa na huci suka kalli juna kai Abidah ta jinjina tana cewa. "Tab dan'kari amma wannan yarinyar anyi tsinanniya tana jinmu fa ta share mu"? Abidah ta fad'a tana sake buga kofa ta d'aga murya sosai tana cewa "zaki bud'e ko kuma saimun karya kofar mun shigo wallahi kika bari muka 6alla kofar nan yau sai mun kusa kashe ki nikam saina 6alla miki qafa" duk abinda suke cewa Ayrah naji tana kuma kallon yadda kofar take rawa tsabar yadda suka girgid'eta wajen bugawa gyara kwanciya ta sakeyi tana ta'be baki domin yau itama fa sun kaita bango ta gaji da abubuwan da suke mata su d'ana cin fuskar da suke mata suji inda dad'i. Sunkai kusan awa guda a gurin suna zaginta da yi mata bala'i da barazana amma bata koda motsa ba balle ta bud'e musu gajiya sukai suka fita suna komawa parlon ganin yadda suke a jigace yasa Hajiya Khubura cewa "ya na ganku haka kamar wanda kukai gudu ina take" zama Nadiya tai Abidah dake tsaye zatai serving d'insu ta cije yatsa tana cewa. "Wallahi Umma yau idan wannan yarinyar ta bari na kamata saina kusan kasheta tsabar duka" "Bata bud'e kofar bane ko Kuma ya naganku babu ita"?. "Ina ta bud'e 'yar gidan tsinannu ko motsinta munji ne balle musa ran zata bud'e mana ai bamu Kai matsayin ba yau haka ta nuna mana" Kai Hajiya Khubura ta jinjina tana cewa "bazan hanaku ba kuci ubanta ku fasa mata jiki ba mai hanaku saboda d'an gadarar nata baya nan dan tselan uwarta har kuje kuna buga mata kofa amma tai banza daku? Humm bari mu gama breakfast d'in nan ku samo mana madoki yau saina 6alle kofar nan da kaina ku shiga ku luguiguita min ita ku tara mata jini a ciki tsabar duka kuma bance ku tausaya mata ba kuyi mata dukan mutuwa ku fasa mata jiki ta yadda gobe idan kuka bata umarni bazata tsallake ba" ta fad'a tana d'aukar spoon suka fara breakfast sai sauri suke su gama su tafi gurin Ayrah su lakad'a mata duka kawai shine burinsu khaleel yana zaune akan kujera a cikin parlor yana jinsu juyawa yai saitin da suke yana kallon Hajiya Khubura yace. "Umma karku ta'ba ta dan Allah bakusan meya hanata fitowa tayi muku ba ya kamata kuyi mata uzuri" ta'be baki Hajiya Khubura tai tana sakar masa harara tace "me kake nufi da muyi mata uziri mu 'kyale ta"? Kaiya d'aga yana cewa 'eh haka nake nufi". "Akan wanne dalili zamu 'kyale ta dan kan uwarta". "Akan na baki ha'kuri Umma karki manta mene Shirin mu a kanta ki tuna idan kuka daketa kamar yadda kike fad'a kuka tara mata jini a ciki ta mutu mune mukai asara kin manta"? Shiru Hajiya Khubura tai domin itafa ta manta cewa ta shirya plan akan khaleel zai aureta daga baya su kashe Daddy su kasheta su mallaki dukiya humm amma fa ta taki sa'a gara daya tuna Mata............... Maganar Nadiya ce ta dawo da ita daga duniyar tunanin data fad'a jin tace "Wallahi Yaya Leel bazamu 'kyale taba yau sai tagane mu taiwa shariya" wani irin kallo yai mata yana jinjina kai yace "dan ubanki dake nake magana koda Umma? Idan na sake jin bakin ki anan saina fasashi wallahi kinsan waye ni ai basai na tuna miki ba ba'ai min katsalandan banzar yarinya kawai" had'e fuska Nadiya tai tana d'auke kai daga saitinsa cikin jin zafin zagin dayai mata akan Ayrah d'in tasa a ranta ko baya nan sai taci uwarta da hankalinta ya kwanta saboda 6ata mata ran dayai kawai tabar cin abincin ta mi'ke tana komawa part d'insu kafin ya fice a gidan taje ga Ayran shima kuma ya kasa ya tsare ya kashewa Abidah warning cewa koda ya fita duk 'yar iskar data ta'ba jikin Ayrah a cikinsu yau baza suyi kwanan dad'i ba, hakan da sukaji ne yasa suka 'kyale Ayrah tilas amma bawai dan sun ha'kura ba sundai rabu da ita a ranar kamar yadda ya bu'kata amma fa duk ranar daya zama baya gida ta kad'e sai sun d'au fansa. 👑Empire👑 Sanin Ahmad baya gari yasa Baby datai sallar asuba jin idonta na rufewa barci bai isheta ba ta koma tai kwanciyarta kafin gari ya karasa wayewa ta tafi school amma har wajen sha d'aya bata farka ba kuma sha biyu da rabi suke da lacture ita Khairat sai karfe biyu zata tafi ganin Babyn ta'ki tashi yasa ta d'an bubbuga ta tana cewa. "Baby ki tashi haka dan Allah gari fa ya waye sosai wato saboda kinga yanxu ya Ahmad baya nan shiyasa sai ayita tashinki kina ji bazaki amsa ba wallahi zanyi miki video a haka na tura masa ya gani nace tunda yabar gida bakya son zuwa school sai ranar da kikaga dama" tana rufe baki a zabure Baby ta tashi zaune ta cilli da bargo kamar bamai barci ba haka ta tashi a wartsake tana cewa "Aunty Khairat so kike ya Ahmad ya kashe ni zaki dau'ki video na ina barcin safe ki tura masa bayan kinsan ya hana mu koma barci idan mukai sallah dan Allah ki goge idan kin d'auke ni" Kai Khairat ta girgiza da murmushi akan fuskarta kamar zataiwa Babyn dariya ganin yadda ta burkice tace "kwantar da hankalinki ban d'auka ba niba waya a guna cewa nayi ki tashi kona d'auka ai kinsan bazan yi miki haka ba indai ba so nake a d'auke ki zuwa asibiti ba" ajiyar zuciya baby ta sauke tana mi'kewa ta sauko qasa ta nufi hanyar toilet tana cewa "kai wallahi har naji dad'i ai nayi tunanin kin d'auka ne shiyasa nabi na susuce bari nayi wanka na fito ko breakfast bazan tsaya yiba saina lalla6a ya Abdul-Hamid ya kaini a hanya ya sai min wani abu naci kawai nasan maybe Ayrah tana can tana jirana tunda nida ita babu me waya kowa kurma ne gara ni nasan hanani akai ita kuwa Ayrah bansan dalili ba ina son ri'ke waya amma boss ya hana". Dariya Khairat tai tana bin bayan Babyn da kallo tace "yakamata idan ya Ahmad ya dawo kisa ya d'auke mu muje gurin sha'katawa irin su eateries mu gano yadda mutane suke harkokin su ko kuma ya kaimu gurin wasannin 'kwallon qafa na stadium mu gano daga can saiki fad'a masa yasai miki wayar Ya kaimu yawon bud'e ido ko? Kai babu ta jinjina tana cewa "Hmm amma ba ya Ähmäd na gidan nan kike nufi ba saidai ya Abdul-Hamid amma indai boss ne saidai ya kaimu yawon duka. "Ba wani yawon duka ki gwada tambaya mana shi tun kafin ya dawo" Kai Baby ta girgiza tana cewa "a'a ba dani ba gad'a maqabarta ki barni kawai jikina ya huta dan nasa a raina bazan sake yin abinda ya Ahmad zai ta'ba lafiyar jikina ba" murmushi Khairat tai tana zama a gefen gadon ta dau'ki littafin da Ahmad ya baiwa Baby tana dubawa har Babyn ta fito ta shirya sannan ta kalli Khairat tana cewa "to Aunty Khairat na tafi ku kam lacture ba yanzu ba yau ko sai karfe biyu"? Kai Khairat ta d'aga tana mi'kewa suka fita tare Mami bata parlor bazai wuce tana part d'in Abbansu ba shiga tai da sallama acan ta sameta bayan sun gaisa ta gaisar da Abban ma ta mi'ke tana yi musu sallama ta fito babu alamar Khairat maybe tayi part d'in Momy books d'in data aje akan hannun kujera ta d'auka tana gyara ratayawar handbag d'inta ta fita a part d'in zata tafi sashin Momy taga prince Hamid dama kuma shi zataje nema da mamaki ya kalleta yaga shirin school tai amma sai yanzu........................... "Yaya Abdul-Hamid ina kwana"? Ta fad'a tana katse masa tunani qara kallonta yai yana cewa "lafiya amma me kike har yanzu baki tafi school d'in ba wato saboda kinsan Ahmad baya gidan ko"? Ya karasa maganar da murmushi kai Baby ta girgiza tana cewa "a'a badan baya nan bane lokacin tafiyar tawa ne bai karaso ba shiyasa ban tafi ba sai yanzu sha biyu muke da class". "Ok yayi aina d'auka ko dalilin kinga gwani baya nan ne" ya fad'a yana shirin wucewa da sauri Baby tace "Yaya Abdul-Hamid" dakatawa yai yana juyowa yace "aha meya faru"? Langwa6ar dakai tayi tana qarqar da murya tace "dama cewa zanyi dan Allah ka kaini school yau idan baka da uziri"? Kallonta yayi sosai yasan abinda bazata iya cewa Ähmäd ba kenan ko iya tsayawa ta kalleshi batai balle ta iya bud'e baki ta fad'a masa cewa ga abinda take so ya tabbata da ace shima Ahmad d'in yana janta jiki ya daina had'e mata fuska ya ri'ka sakewa ko kad'an ne da ita dan ta saba dashi amma ina ya kasa yai hakan....................... "Ya Abdul-Hamid". Maganar datai yasa ya dawo daga tunanin da yake ya kalleta zaiyi magana tace "ko kana da aiki"? Kaiya jinjina yana cewa "eh akwai amma muje na kaiki yau ba hospital zanje ba airport zanje karfe biyar da rabi". "Airport kuma yaya Abdul-Hamid wa zaka d'auko". "Wani ne muje na kaiki kekam ba ruwanki da wanda zanje d'aukowa" dariya Baby tai tana cewa "to kodai budurwarka zaka d'auko shiyasa baka so mu sani"? Kaiya d'aga yana murmushi yace "eh kamar kin sani ita zan d'auko" ya fad'a yana wucewa gaba tabi bayansa tana sake tambayarsa. "Yaya Abdul-Hamid baka fad'a min a ina take ba mene sunanta"? Daidai sun isa wajen da motocin masarautar suke yasa key yana bud'e murfin motar ya shiga zagayawa itama tai tana shiga ya tada mota suka bar masarautar Baby kam bata ha'kura ba a hanya ma saida ta sake tambayarsa "Yaya Abdul-Hamid baka fad'a min a ina take ba mene sunanta"? Jin abinda ta sake fad'a yasa ya kalleta yana murmushi yace "sunanta mele" a shagwa'be Baby tace "kai Yaya dan Allah ka fad'a min". "Amma baby zaki iya tarar Ahmad da irin wannan maganar ko ki tambaye shi kamar yadda ni kike min yanzu"? Zaro ido tai tana girgiza kai tace "niii wanne tsautsayin ne zaisa na tari ya Ähmäd da irin wannan tambayar humm aiko ranar dana kwana a asibiti dan nasan bazai ta'ba 'kyale niba". "Ok ashe kura tasan gidan me babban sanda kenan saboda kinga ni bana fad'a shiyasa kika dameni da tambayar ko "?. "A'a kawai dai naji dad'i ne da naji kana da budurwa muma kwanan nan zamu samu Aunty mu ri'ka zuwa gurin ta ziyara". "A'a ba kwanan nan ba Baby sai nan gaba sosai ba yanzu zanyi aure ba dan sai Ahmad ya rigani ma". Da mamaki Baby tace "Ya Ahmad kuma shi d'in yana da budurwa ne dama bamu ta'ba sani ba"?. "Eh yana da ita man baki sani ba"? Kaita d'aga tana cewa "nikam ban sani ba saifa yau taya zan sani bayan ko fuskar gaida dashi bama samu sosai fad'an sa yafi shirunsa yawa amma koba komai nasan yanzu zamu huta da yayi aure shikenan zai d'auke hankalinsa a kanmu ya mayar kan matarsa" kai prince Hamid ya jinjina a ransa yana hasko daya za'ai ta sani zaman me ake dahar yanzu ba'a fad'a mata ba to sai yaushe ya kamata ace lokaci yayi da zata sani shi kansa Ahmad daya fahimci tasan cewa shi yake sonta zai aureta maybe daga ranar zai daina mata abubuwan da yake mata..................... "Yaya Abdul-Hamid yaufa banyi breakfast ba dama nace sai zaka kawoni ka sai mun wani abu" daina tunanin da yake yayi yana kallon ta yace "ok me kike so"?. "Ina son ice cream da chocolate kawai idan na dawo gida naci abinci". "Amma da kin fad'i wani abu me kyau kyace a siya miki kayan sanyi bakya tsoron mura ta kamaki"? Fad'i wani dai amma Banda wannan a marairaice Baby tace "dan Allah Yaya Abdul-Hamid shi nake so please" parking yai yana cewa "ok jirani" ya fad'a yana fita tana zaune ya sayo mata ya dawo suka karasa school d'in ya sau'keta tai masa godiya sosai cikin jin dad'i saidai tayi mamaki da bataga Ayrah ba kardai bata zo ba meyasa yau tayi fashin school kalle kalle ta fara ganin babu alamarta yasa ta karasa shiga cikin class d'in nasu a zaune taga Ayran da book a gabanta tana karatu sauke numfashi tai tana karasawa ta dafata tana cewa "Ayrah Abdul-Kharim yakike kwana biyu"? D'agowa Ayrah tai ganin Baby yasa tai murmushi tana ri'ke hannunta tace "kai oyoyo Zuhra Ashraf Sharfaddeen ai tun d'azu nake jiran zuwanki naga shiru baki zo ba ya akai"? Zama Baby tai tana aje littafan hannunta da ledar da prince Hamid ya sayo mata kayayyi tace "humm kedai bari kawai Ayrah inacan a gida Ina shirgar barci saboda boss baya nan yabar gari". "Kema yayanki yabar gari Ashraf Sharfa kice hutu kike abinki"?. "Uhm nikam hutu nake wallahi ranar daya tafi kamar sallah har party muka had'a nida Aunty Khairat da Sultan" kai Ayrah ta jinjina tana cewa "nikam nawa Yayan daya tafi ranar wuni nayi ina kuka karshe har zazza'bi nayi gashi 'yar wayar da zamu ri'ka magana ma bani da ita". "Ok ayya yayanki Aiman kema ya tafi ne"? Kai Ayrah ta d'aga Baby taci gaba "wacce qasa ya tafi"?. "Beijing" . "Allah ya dawo dashi lafiya". "Amin Zuhra na gode" ta fad'a jiki a sanyaye bud'e ledar shopping d'in da prince Hamid yai mata l kallon Ayrah tai ganin yadda tai shiru kamar tana cikin damuwa tace "Ayrah meya faru naga fuskarki kamar da matsala"? Murmushi Ayrah ta saki wanda iyakacin sa kan le6enta saboda kartasa Babyn a damuwa tace. "Babu komai Zuhra kawai ina tunanin tafiyar ya Aiman ne shiyasa". "Uhmm 'kwarai kekam har jin kewar yayanki kike banda mu mukam farin cikin fecewarsa muke". "Aini dole nayi kewarsa saboda shine komai nawa shine yake kula dani" tashi Baby tai tana cewa "ok ayya Allah sarki Ayrah karki damu insha Allahu zai dawo ai kamar yaune taho muje waje musha wannan dan haka na taho banci komai ba" mi'kewa Ayrah tai suna fita inda suka saba zama anan suka zauna sunaci gaba da hirarsu har lokacin shiga lecture d'insu yayi suka shiga awa uku bayan sun fito Baby taiwa Ayrah sallama driver yazo d'aukarta suka tafi Ayrah itama ta kama hanya da yake kullum a kafa take zuwa ta koma a kafa Hajiya Khubura bata ta'ba bari Daddy ya baiwa Ayrah kud'i wanda zata hau napep koda naira biyar ne bs ada kuma kafin ya sauya driver ya aje mata yake kaita wani lokacin kuma da kansa yake kawota har cikin school lokacin tashi ya baro office d'insa yazo ya d'auketa ya mayar da ita gida tsabar gata baya bari tai tu'ki da kanta amma yanzu ko kallo bata ishe shiba saidai tasan ba laifinsa bane tabbas akwai lauje cikin nad'i shiyasa ta daina damuwa da halin ko in kula d'in da yake nuna mata tasani wata rana sai labari komai zaizo ya wuce kamar ba'ai ba. Baby ta riga Khairat dawowa gida dan ita sai jikin magriba sosai ta dawo direct part d'in Mami ta wuce dan a 6angaren Mamin suke yanzu kafin su koma na Momy tana shiga taga Baby a zaune ita kad'ai a bedroom zama tai cike da gajiya tana cire hijab d'in jikinta ta aje a gefe kafin ta sauke numfashi tana kallon Babyn tace "Baby kinsan wana gani a harabar gida yanzu sun tafi masallaci da yaya Abdul-Hamid kuwa"? Khairat ta fad'a tana zaro ido tare da ri'ke baki" kai Baby ta girgiza tana cewa "a'a waye a wajen dama Yaya Abdul-Hamid d'azu yace min budurwarsa zaije ya d'auko a airport". Gwalo ido waje Khairat tai tana cewa "wacce irin budurwar tasa hum'um to wallahi ya Ahmad ya d'auko ba wata budurwa Yaya Abdul-Hamid d'in ne yake da budurwa boss ne ya dawo"? Zaro ido waje Baby tai itama jin abinda Khairat tace harda zabura tana mi'kewa tsaye tana cewa "Aunty Khairat kikace Ya Ahmad ya dawo kuma dama ba dad'ewa zaiyi ba ko kuwa hukunta ni ya dawo yi"? Ta fad'a tana d'ora hannu aka. "A'a akwai abinda yazo yi inaga karma ki d'orawa kanki wata damuwa ko tsarguwar danke ya dawo ko d'aya ba lallai hakan bane tunda naji Abba suna maganar da Momy dazu bayan tafiyar ki school naji abbanmu yana cewa zai dawo yau akwai abinda zaiyi bazai wuce sati biyu ba zai koma" sauke numfashi Baby tai jin abinda Khairat tace tana cewa "kai Masha Allah har naji dad'i wallahi Allah yasa idan mun had'u karyai min magana akan abinda ya faru". Da sauri Khairat tace "Allah yasa kar yai mana magana dai kin manta Nima harda ni". "Uhmm Aunty Khairat naki me sau'ki ne nifa kinsan abun biyu ya had'e mun yace idan ya dawo saina gane Allah da girma yake nidai na shigesu na da azaba ya Allah ga baiwarka tana cikin matsala ka cireta daga tarkon bawan nan naka" ta fad'a tana bud'e hannu Amin Khairat tace tana dariya ta mi'ke tana shiga toilet zatayo alwala yayin da Baby tai zaman dirshan tana rafka tagumi kafin Khairat d'in ta fito. A ranar basu yarda sunje part d'in Momy ba saboda kowa tsoron had'uwarsa da Ahmad yake musamman Baby a ankare take ta kasa sakewa hatta abinci da Khairat ta fita ta d'ebo musu da'kyar taci baifi spoon biyar ba tasha ruwa kawai ta sakawa kofar bedroom d'insu lock suka kwanta duk da haka saida Khairat ta riga Baby barci saboda yadda ta saka dawowar Ahmad d'in a ranta kasa runtsawa tai data rufe ido take ganinsa saidai ta bud'e da sauri ta kama waige-waige har jikin asuba idonta biyu barci 6arawo shiya d'auke ta batare data sani ba kuma da asuba ta riga Khairat tashi tai sallah bata iya komawa ta kwanta ba taci gaba da zama akan sallaya tana addu'a har Khairat itama ta tashi ta sallar saidai ita tana idarwa ta mi'ke ta koma gado kallonta Baby tai tana cewa "Aunty Khairat kin manta ya Ahmad ya dawo wai barci zaki koma"? D'agowa Khairat tai zatai magana ganin yadda idon Babyn yake yasa tace. "Baby kiga yadda idonki yayi ja baki samu isasshiyan barci bane kome hakan" kai Baby ta jinjina tana cewa "Humm Aunty Khairat kedai bari kawai ban samu na iya barcin ba sai wajen asuba shiyasa kika ganni haka" da mamaki Khairat tace "saboda me"?. "Kin manta ya kashe min warning kuma yace idan ya dawo zamu gauraya tuna hakan yasa na kasa sukuni har karfe uku da rabi bansan sanda barcin ya d'auke ni". Murmushi Khairat tai tana cewa "ai kuma kinsan duk rintsi ya Ahmad bazai shigo mana ba bedroom da dare ba dakamar da safene da yanzu kin ganshi idan yayi niyya Baby ki cire wannan tsoro da damuwar a ranki ki sallama kinsan ya Ahmad idan yai ra'ayin abu sai yayi dan haka ni banga wani abun ki d'aga hankalinki ba tunda kinsan kome zaki idan yaga damar ya hukunta ki zaiyi toni anan banga abinda zaisa ki takurawa kanki ba" sauke numfashi Baby tai tana kallon kofar bedroom d'insu kafin ta d'an girgiza kai tana cewa. "Shikenan Aunty Khairat nagode zanyi kokari naga nayi yadda kikace min da ace abinda kika fad'a min zan iyayi dani kaina na huta amma zan gwada" kallonta Khairat tai tana sakin dariya tace "to indai haka ne tashi muje part d'in Momy nasan yana can ki dake karki nuna wani abu kamar yadda nima zan tsume idan yaga haka ina mai tabbatar miki maybe bazai tada mana wancan zancen had'a partyn da mukai ba. "To Kuma Aunty Khairat kin manta nifa yanzu ba wannan ne a raina ba cewa dayai zan gane ya aje waya na ta'ba masa wannan shine matsala ta". "Ki had'a harda wannan laifin da kikai masa duk ki share muje kawai Khairat ta fad'a tana ri'ke hannunta alamar ta tashi su tafi Baby batako motsa ba sai tambaya data jefo mata "anya kina ganin zan iya kuwa"? Kai Khairat ta d'aga tana cewa "kwarai zaki iya saidai idan bakiga dama ba shimafa mutum ne kamar mu taso kawai kinsan indai Momy ko Yaya Abdul-Hamid wani yana nan bazasu bari ya dakemu ko yasaka mu wani abu me wuya ba" shiru Baby tai kamar zatai kuka tace. "Nidai kawai kije banda ni basai naje ba". "Ban gane basai kinje ba? Please Baby taso muje nayi miki alkawarin koda ace zaiyi tambaya zan bashi amsa kozai dakeni zan shiga cikin zancen ku inyaso ya had'a mu tare yayi mana komai" jin abinda Khairat tace yasa baby d'agowa ta kalleta sosai tana cewa "Aunty Khairat da gaske bazaki barni ni kad'ai ba"?. "Da gaske man Baby taso muje" mi'kewa Baby tai zuciyarta na harbawa tana dar-d'ar suka nufi 6angaren Momy suna shiga kuwa dashi suka fara had'a ido yana zaune kusa Momy suna zance tsaye sukai a kofar shigowa aka rasa wacce zata fara shiga kowa sai raba ido take kamar Ahmad bai gansu ba ya sharesu yaga iya gudun ruwansu aiko kusan awa guda suna tsaye kaiya jinjina a ransa yana fad'in lallai yaran nan basu sanni ba har yanzu amma zanyi maganin ku d'agowa yai yana kallonsu daidai Momy ta mi'ke ta shiga bedroom sakamakon wayarta da aka kira kusan numfashin sune yaso d'aukewa ganin wacce zata taimakesu tasa baki tabar gurin su juya yaci ubansu su karaso nan yaci ubansu ko'ina basha.................. "Kai tsaiwar me kuke anan ku karaso min kafin sakan daya bana son taku duk wacce ta taka zan take ta" tun bai gama magana ba da gudu suka karaso kowa jiki na 6ari musamman Baby da taga ita yafi kallo tasan yau kam Allah ne kad'ai gatanta........... Saukar muryasa sukaji yace "Baby da Khairat wato saboda na tafi shine kuka had'a party ko harda gabatarwa da DJ nagode gani na dawo ba tafiya nayi har abada ba saidai ku sani yau kun shiga uku sai kun sake had'a min valentine day kamar yadda kuka had'a ranar ku tashi ku nemo cake duk inda yake da balloons sannan ku aro mp dakuka aro nima ina so kuyi min a fili In gani" ya fad'a fuskarsa a had'e yana kallonsu babu ko d'igon murmushi da ganin yanayin sa babu sau'ki tsabar yadda suka rud'e babu wacce fuskarta babu hawaye jiki kuma na rawa ganin halin tashin hankalin da suke ciki yace. "Ko ban kai matsayin da zakuyi min ba"? Duk shiru sukai wanda zai girgiza kai ma a cikinsu rasawa akai sai kuka da yazo musu shima kuma an rasa wacce zata fara fito da nata fili ganin sunyi tsit yasa cikin tsawa yace "ko baza kuyi ba yanzun nan jikin ku yai tsami wallahi yau sai naci ubanku" jin abinda yace yasa Baby kukanta ya fito fili dan tasan duk tsiya kome zaiyi musu saiya fara 'kyale Khairat kafin ita.................... "Ke wato harkin samu bakin kuka ko? Yayi kyau ku tashi ku fara kar'bar hukunci zakuga karshen azabata yau ku fara zaga min parlon nan da frog jump" yana rufe baki da sauri suka tashi kowa ta ri'ke kunne suka fara duk girman parlon da yawan kujerun sai sun zagaye su kuma babu hutu yana kallon su da yadda suka gaji amma yai banza dan yasa a ransa daga yau bazasu sake marmarin koda dariya bane idan ya tafi, suma a nasu 6angaren sun d'auka abun nasa da sau'ki amma sai sukaga baida alamar cewa su tsaya gashi Momy kamar bata part d'in har lokacin bata fito ba tsabar wahala kukan ma sun daina idonsu ya bushe. "Ku tsaya". Yana fad'a da sauri kowa ta tsaya a inda take tare dayin zama da6as suna mayar da numfashi tabbas sun sha wahala ko yanzu ya barsu sun azabtu mi'kewa yai batare daya kalli inda suke ba ya nufi hanyar fita yana cewa. "Ku biyo ni". Zaro ido waje sukai musamman Baby da taji cinyarta kamar ba'a jikinta take ba gashi harya fita mi'kewa Khairat tai da'kyar hajijiya na d'ibanta ta kalli Baby tana cewa "Baby taso mu tafi kinsan ya Ahmad yana da sauri maybe yanzu yaje part d'insu fa karmu jawowa kanmu duka bayan wannan azabar" numfashi Baby ta sau'ke hawaye na zubo mata zurr kafin itama ta rarrafa ta dafe kujera tana runtse ido da'kyar ta samu ta mi'ke kowa tana jan'kafa suka fita yadda suke jin ciwon jikinsu babu me iya sauri a cikin su dole sai a hankali suke tafiya har suka shiga part d'in nasa yana zaune sukaje da suka karasa inda yake kowa kasa dur'kusawa tai. "Bazaku iya zama bane? Ya tambaya yana kallon su "ai bakuji komai ba kuma bakuyi nadama ba tunda har zanyi tafiya bayan kunsan waye ni dan rainin hankali har ku zauna kuna d'aura balloons da sayo cake kuyi party saboda mugu yabar gida ko? Yau kuwa zakuga mugu zanyi maganin ku" ya karasa maganar yana mi'kewa yace "ku biyo ni" kallon juna sukai a matukar razane yaufa sukam sun shiga uku ina kuma zai kaisu ina zasu sake binsa......................... Sautin bud'e kofa ne ya dawo dasu hayyacinsu ganin ya bud'e ya fita suma suka bi bayansa garden ya shiga yana tsayawa a gurin fountain bai juyo ya kallesu ba yace "Khairat d'auko min boket guda biyu a bathroom d'ina minti d'aya na baki" jin abinda yace yasa Baby sake susucewa mezai saka su badai d'iban ruwa ba Allah yasa Khairat ta had'u da prince Hamid ya tambaye ta me zatai da boket ko Allah zai taimake su................ Ganin Khairat d'in ta dawo da botikan biyu a hannunta yasa Baby ta fahimci basu had'u dashi ba kawowa tai tun kafin ta ajiye yace "dau'ki d'aya ki baiwa Baby d'aya ku fara d'iban ruwa kuna bin flower's d'in nan kuna zuba musu ruwa yau sai kun wuni kuna watering idan tsautsayi yasa na dawo na tarar bakwa sauri ko kun tsaya hummmmnn" yana fad'in haka ya juya yabar gurin kallon juna sukai Khairat data dafe kanta daya sara tace. "Mun shiga uku mune zamuyi watering din flowers yau innalillahi wa inna ilaihi raji'un wallahi a yanxu ma bakiji yadda nake jin jikina ba balle nazo nayita jidon ruwa ina bin flower d'aya bayan daya ina zubawa"? Numfashi Baby kawai ta sauke tana cewa "dan Allah Aunty Khairat mu fara karya dawo ya tararmu a tsaye kinsan halinsa abinda zaiyi mana bazai kyau ba" ta fad'a tana wucewa tasa boket d'in ta d'iba karasowa Khairat tai itama ta d'iba suka fara bi suna zubawa saboda tsoron kar yana kallon su yasa ko iya tsayawa basayi. Ahmad kam kwata-kwata ma baya part d'in ya koma gurin Momy sunci gaba da maganar da suke kamar baisa su Baby komai ba itama Momyn bata tambaye shi inda suke ba duk zatonta ko lokacin data tashi amsa waya su kuma suka fita batasan suna can sun zama masu bayin fulawa ba ya 6ata lokaci sosai a gurinta kafin ya tashi ya koma part d'insu yana shiga ya bud'e kofar da zata kaishi garden ya fita tsaye yayi yana kallon su yadda duk suka bi suka ji'ke da ruwa Allah sarki bayin Allah babu wacce take iya magana a cikinsu kawai aiki suke cike da tsananin gajiya kaiya jinjina yana karasawa inda suke duk da haka basu lura dashi ba saida sukaji gyaran muryarsa a d'ari kowacce ta zabura suka juyo kallon tsaf ya sake yi musu kafin yace. "Tunda na tafi iya abinda kukai kenan baifi guda d'ari kuka zubawa ruwa ba"? Jin abinda yace yasa kowacce mamaki ya kamata badan kar suyi 'karya ba sai suce duk flowers d'in dake garden d'in nan sun bata ruwa saidai wacce bata fito ba amma yace iya aikin da sukai kenan tunda ya tafi babu wanda tai zaman hutun minti d'aya a cikinsu saboda tsoron karya dawo ya same su................... "Ok babu me iya bani amsa a cikinku saboda kun cika ko? Shikenan Kuci gaba da aikin dama aina fad'a muku yau wuni zakuyi kuna kar'bar punishment har dare ku d'ora inda kuka tsaya domin yanzu karfe d'aya da rabi tai" yana rufe baki Baby ta fashe da kukan tsantsan wuya da gajiya tana dur'kusawa a gabansa tare da had'e hannuwanta tace "dan girman Allah Yaya Ahmad Kayi hakuri ka yafe mana mun aikata kuskure wallahi tallahi bazamu sake ba dan Allah kayi ha'kuri" jin abinda tace maimakon ya kar'bi ban ha'kurin ta saiya sake had'e rai yana kallon Khairat wacce ke tsaye tana mayar da numfashi yace. "Wato ke kinfi karfin ki bada ha'kurin ko? Yau kuwa bazaki bar garden d'in nan ba ke kwana zakiyi kina baiwa 'kananun tsirrai ruwa zakisan dani kike wasan............ Da gudu itama Khairat ta dur'kusa tana cewa "a'a wallahi ba haka bane Yaya Ahmad dan Allah kayi mana afuwa kayi ha'kuri wallahi mun dau'ki alkawari bazamu sake ba daga yau". "Kuma sake man ina daidai daku nine maganin ku a gidan nan ku tashi ku 6ace min da gani" yana rufe baki suka mi'ke a susuce kowa tana neman hanyar gudu kamar zasu tashi sama fiiiiiiii haka suka fita da'kyar suka iya kai kansu part d'in Momy badon tsoron karya biyo bayansu ba dasun tsaya sun yiwa driver magana ya kawosu amma gara koda rarrafe ne suje a hakan da muguwar rawa gara 'kin tashi. A gigice suka shiga suna huci kowacce ta zube akan kujera da mamaki Momy take kallonsu ganin babu me cikakkiyar nutsuwa a cikinsu tace ''ku kuma daga Ina kamar wanda kukai wasan ruwa duk kun ji'ke jikinku gashi kunyi wani iri kamar marasa lafiya daga ina kuke yanzun bayan zan shiga amsa waya na ganku kun shigo"?. Kallon kofar shigowa Khairat tai zatai magana kawai saiga hawayen wahala da'kyar tace "Yaya Ahmad ne ya sakamu watering a garden tun d'azu da muka shigo bayan an kiraki a waya kin shiga part d'inki" da sabon mamaki Momy ta sake kallonsu tana cewa "ya sakaku watering kuma na tsawon wannan lokacin me kukai masa haka bayan shigowar ku part d'in kenan"?. "Momy tsohon zance ne akan partyn da muka had'a na tafiyar dayai ne shine yace gaba ma mu sake yana daidai damu dan baki fito da wuri bane anan parlon ya fara saka mu tsallan kwad'o bayan mun gama ya kaimu garden mukai watering d'in". "To Allah me iko akan haka ya sakaku wannan azabar kalli yadda kuka koma aini ban sani ba da yanzu naje na taho daku kuma Abdul-Hamid ma inaga baya nan shiyasa da ace yana nan bazai bari kuyi watering ba tunda kuba gardener bane gashi ya saka min ku shan wahala musamman ma ke Baby kalli yadda kike rawar d'ari ko magana kin kasa gara Khairat d'inma da d'an sauran 'karfinta ku tashi ku shiga bedroom kowa ta cire kayan kuyi wanka da ruwa me zafi sosai saiku fito ku had'a tea kusha zaku samu d'umin jiki sosai tashi kuje" mi'kewa sukai kowa najan kafa suka shiga part d'insu da'kyar sukai wankan amma a cikinsu babu wacce ta samu damar fitowa tasha tea d'in balle suci abinci duk kwanciya sukai ganin shiru basu fito ba yasa Momy tashi tabi bayansu data bud'e kofar bedroom d'insu ganinsu a kwance yasa batai magana ba ta mayar ta rufe flask ta d'auko ta dawo tana had'a musu ta baiwa kowa sannan ta koma ta sake had'o musu abinci ta kawo tasa su gaba saida sukaci Baby kam tuni zazza'bi ya rufeta sosai Khairat d'in ma jikinta yad'au zafi kamar wuta ganin haka yasa ta d'auko musu magani kowa ta 6alla tasha suka tashi sukai sallah a daddafe domin tafiya ma ko d'an kaciya bazai fad'a musu ba haka suke takawa sunayin sallar kuwa suke sake kwanciya kowa idonta biyu amma bamai magana a cikinsu saidai saukar numfashin juna kad'ai suke ji a haka har akai la'asar da magriba da isha duk saidai su tashi suyi sallah kawai su koma kwanciya babu wacce zata moru a cikin su dai a wannan ranar. Ahmad kam bai sake shigowa part d'in Momy ba sai wajen qarfe tara da rabi yana zuwa kuwa ta balbaleshi da fad'a sosai ta nuna masa bai kyauta ba abinda yayi musu da nasan suna part d'insa lokacin daya dawo suke magana wallahi da taje ta taho dasu kashe mata 'yan matan nata yake son yi ko kuma yaya dazai ri'ka basu wahala haka Ahmad dai shuri yayi yana sauraron ta saida takai karshe ya bata hakuri ya nuna bazai sake irin hakan ba kafin ya mi'ke yana fita a part d'in ya koma nasa ya d'auko alluran zazza'bi ya dawo Momy bata parlor direct part d'in su Khairat ya shiga suna kwance kowacce tayi barci kunna fitilar wayarsa yayi yana haskasu ganin barci suke ya yaye bargon da suka lullu'ba yasa hannu ya dafa goshin Khairat yaji jikinta babu zafi site d'in da Baby take kwance ya koma itama ya dafa nata goshin kamar na Khairat d'in itama zazza'bin ya sauka mayar musu da bedsheet d'in yayi yadda yake ya rufesu yana fita a part dama so yake yaji inda me zazza'bi yayi musu allura karsu kwana da zafin jiki amma tunda duk ya sauka shikenan nan..............✍️Mrs Äl'ämëëñ Ahmad ce. TYPING 📲Tue, Apr 1/25 10:00AM YUSRAH MUSA ABUBAKAR 🤘💯. 👑 ROYALTY 👑 ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫 Home of hospitality and harmony gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai 'ya'yan ta. ••••Dedicated to my blood•••• SALEEM MUSA ABUBAKAR NAJA'AT MUSA ABUBAKAR FATIMA MUSA ABUBAKAR AISHAT MUSA ABUBAKAR ABUBAKAR MUSA ABUBAKAR √Wannan page din naku ne yan uwa rabin jiki Allah ya bamu ha'kurin rashin mahaifin mu ubangiji ya gafarta masa yayi masa rahma ya haskaka kabarinsa. ANNABI SAW Annabi farkon kasantattu wallahi ubangida ba danka ba daba abinda zai wanzu. Da sunan Wanda ke rayuwa me tasiri darai dubba ma'kagin duj abunda baza'a kirashi da rabbi Allah ba nagode ma da sigar dazan banma ko furta uffan ba da kaban iko nake wake wanda kace kadarinsa ya wanzu. 10~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Raki'inah. @YUSRAHMS CE Page 19 & 20 Duk wani shiri da Hajiya Khubura zasuyi na biki sun gama Daddy yana shan kallonsu baice musu komai ba iya abinda ya kamata ace yayi matsayin sa na mijin Hajiya Khubura kuma zatai auren 'ya ya bata gudun mawa me yawa sosai da kud'i da kayayyaki a take ta saka kud'in cikin account d'inta sannan da wayo ta sake fad'a masa cewa abubuwan da zatai bata gamaba kud'in sun qare ya sake mata transfer wasu a take murna kuwa harda rawa. A 6angaren Nadiya masai gyare gyare ake kullum ba zama ita da Abidah suyi nan suyi can khaleel kuma baya gidan kwana biyu yaje gidansu sai daren d'aurin aure zai dawo domin fushi ya d'auka da Hajiya Khubura ya fad'a mata yana son a had'a aurensa da Ayrah dana Nadiya tace a'a shi ba yanzu ba akan haka yai yaji ya tafi ko kiranta a waya bayayi idan ta kirashi baya d'auka karshe dole ta 'kyale shi tasa a ranta duk inda ya tafi ma yana gama hucewa daga fushin zai dawo ya sameta tana zaune itace ta haifeshi ko shine ya haifeta dazai ri'ka juyata kamar wata uwar wofi. Yadda gabadaya suka d'au busy yasa yanxu Ayrah tad'an samu hutu basa bi takanta suna harkokinsu basa sakata aikin komai ko wata takura kowacce rana da inda zasu je basa samun wuni a gida ita kuwa koda yaushe tana bedroom d'inta idan kaga ta fito tofa saidai idan kitchen zataje ta d'ebo abinci ko kuma zatai wani aikin amma haka kawai dai bata fitowa gudun karma su ganta suci gaba da azabtar da ita daga inda suka tsaya addu'a take kullum ba dare ba rana tana fatan Allah ya baiwa Abidah mijin aure itama ta samu tabar gidan tasan ko iyasu ta rabu da jarabarsu zata huta saura khaleel shiko tunda namiji ne babu inda zaije saidai tai addu'ar neman tsari daga sharrinsa dan tunda dad'ewa ta gama karantarsa da halayensa d'an iska ne iya kallon da yake mata ya isheta hujja. ****Mama batasan Ahmad ya dawo gida zaiyi uziri na d'an wani lokaci ba saida sukai waya da Momy take iyota tana tambayar ina Ahmad soja marmari daga nesa Momy take fad'a mata ai ya dawo gida ma zaiyi wani abu ne amma dai ba wata dad'ewa zaiyi ba zai koma hum jin haka yasa tunda suka gama wayar Mama ta kasa nutsuwa tasa tunanin ta waje d'aya sai kaiwa take tana komowa ta kira Maryam a waya yafi sau goma bata d'aga ba kamar tai kuka sai huci take tana cizon yatsa ta yarfa hannu ta le'ka harabar gida tana cikin wannan yanayin Maryam ta dawo daga school tana shigowa ganin yadda Maman take a hargitse yasa ta dakata tana cewa. "Mama lafiya na ganki haka wani abune ya faru"? Tsayawa guri d'aya Mama tai tana sau'ke numfashi tare da girgiza kai tace "Maryam me kike kallo ne Anya burinmu zai cika kuwa kin tsaya wannan sakarcin ace ni harna fiki damuwa da saka abun a rai inaga kullum sai nayi mafarki akan haka amma naga ke ko a jikinki haba Maryam kinyi hauka ne so kike kisa hawan jini ya kamani"? Cikin rashin fahimta maryam tace. "Ban gane ba Mama dan Allah kiyi min bayani yadda zan fahimci inda kika dosa me nayi ne bansan akan me kike magana ba kin sakani a duhu'. Zama Mama tai tana had'e hannunta guri d'aya ta dafe goshi tana cewa "magana nake akan Ahmad ya dawo yau kusan kwanansa shida amma ban samu labari ba sai d'azu Aunty ta kirani kamar wasa nake tambayar sa dan naji yaya sai tace min wai ya dawo zaiyi wani uziri ne ya koma". Zaro ido Maryam tai tana cewa "ya dawo kuma Mama da gaske ne yanzu yana gari yana masarauta idan naje zan ganshi"?. "Yana nan man tunda kikaji ta fad'a nikam indai a haka zamu tafi bana hango nasara a tare damu". "A'a Mama ba haka bane nifa bansan ya dawo ba amma yadda nake sonshi kinsan bazanyi sanya ba yanzu ma lokaci bai 'kure min ba a raina nasa saina auri Ahmad kuma insha Allahu saina aureshi na zauna dashi na har abada koda ace mata uku yake dasu indai ya amince min zan yarda na shiga matsayin ta hud'u" Maryam na rufe baki Mama tace "ai Maryam ko mata hud'u ne dashi yace yana sonki wallahi sai kin aureshi inyaso saiki zauna matsayin 'kwar'kwara nidai damuwata kawai ki aureshi ace 'yata ta cikina dana haifa tana auren jinin sarauta an gama magana hakane burina". "To amma Mama ya zanyi kinsan fa dole sai nad'au salo sakamakon nasan halin Ahmad tunba yauba akwai rainin wayo magana ma idan kikai masa sai yaga dama zai amsa miki balle naje a fuskar sonsa nake da aure duk ranar daya fahimci hakan nasan zansha wula'kanci ba 'karami ba" ta'be baki Mama tai tana kallon yadda Maryam d'in tai shiru tana kallon guri d'aya alamar tunani tace. "Idan kin sone zai wulakanta ki sabida kince kina sonsa bai isa yace zai nuna miki gadara ko wani abu ba shifa namiji ne duk matsayin sa da mu'kaminsa dole ya lallashi mace ya lalla6ata kamar 'kwai koda ace itace ta fara cewa tana sonshi kin gane"? Kai Maryam ta jinjina tana cewa "eh Mama na gane to amma yaushe zanje"?. "Yau mana Maryam dake nufin ki sai yaushe zakije saiya tafi kome haba Maryam anya kina jin yadda nake ji a raina kuwa inaga harna fiki shiga damuwa da son naga wannan abun ya zamu gaskiya bari kiji ko barci bana iya samu nayi cikakke me kyau saboda saka abun a raina danai nida nake ta dakon dawowarsa dama kamar na jawo iya adadin dad'ewar da zaiyi acan ya dawo haka nake ji tashi ki shirya yanxun nan ki tafi kawai karki d'ebi kaya masu yawa saboda kar aga haukanki ki dau'ki ko kala biyu ma" mi'kewa maryam tai tana cewa "ok bari naje na shirya" ta fad'a tana wucewa ko tsayawa wanka batai ba iya kayanta ta d'auko ta sauyo mayafi ta fito har lokacin Mama tana inda ta barta ganin ta fito yasa ta kalleta baki bud'e tana cewa. "Na shiga uku Maryam ya haka tun daga yanxu zaki fara kuskurewa"? Kallon jikinta Maryam tai tana cewa "mena kuskure "? Fuskarta Mama ta nuna tana cewa "a haka zaki tafi gidan kamar wacce take takaba ko d'an kwalli babu balle jan baki ko powder? aiko indai haka xakije kiyi wallahi Ina me baki albishir ko kallonki Ahmad bazai ba dole sai kina d'aukar wankan kece raini wanda idan kika fito baisan lokacin dazai biki da kallo ba ki ri'ka karya harshe wajen magana idan kinga yana kallonki ko hankalinsa yana kanki ki ri'ka abunda zaki burgeshi idan kun kad'aita ku biyu kiyi iya kokarinki ki nuna masa 'yar wata alama dazai fahimci kina sonsa ko baki furta ba ya sani daga nan idan mukai sa'a saidai kiji yace yana sonki". Murmushi Maryam tana hasko irin yadda zataji a ranta duk ranar da taji Ahmad ya furta Mata kalmar so humm ranar mutuwa ne kawai bazatai ba tsabar farin cikin da zata tsinci kanta a ciki...... "Maryam baki ce komai ba sai iya murmushi naga kinyi"? Kallon Mama Maryam tai tana jinjina kai tace "karki damu Mama ni nayi miki alkawarin shawo kan Ahmad cikin sassau'kan hanya a d'an karami lokacin da zanyi ina tabbatar miki bazan dawo gidan nan ba saida amincewar yana sona zai aureni na tafi Mama ki taya ni da addu'a" ta fad'a tana juyawa zata fita a parlon jawota baya Mama tai tana cewa. "Please Maryam ki tsaya ki nutsu kiyi amfani da kyawawan kalamai ke mace ce kinsan abubuwan da zaki ri'ka yi wanda zai burgeshi ki jawo hankalin sa kanki da wuri dan Allah ba shashanci nace kije kiyi ba ki kokari kiyi abinda ya kaiki gidan kawai shine abinda ya kamata kiyi ba shirme ba''. "Insha Allahu Mama karki damu nimafa ina zumud'in wannan al'amarin taya zanyi sake na bari har na samu damar zama dashi na kasa jan hankalinsa gareni kamar ba mace ba indai dan soyayyar Ahmad ne karki damu ki ri'ka sakawa a ranki kamar na aureshi ne anyi komai an gama jira dai ba yanzu zanje gidan ba? Humm muje zuwa shiri nagaba saina jiki a waya" murmushi Mama ta saki tana cewa "yauwa Maryam insha Allahu zaki nasara sai kin auri Ahmad domin kullum bana barcin kirki ina tsayuwa sallar dare saboda kicika burinki nima nawa ya cikana ganin na had'a jini da sarakai wata rana na bud'e ido naga jikanu na sune a fada hummm abun zaiyi matukar kyau koba fad'a ba". "Tabbas zaiyi kyau Mama nasan addu'ar ki zatai min amfani sosai dan Allah karki daina kici gaba da yimin nasan zan samu kan Ahmad ya aure ni da sauri saboda addu'ar iyaye ga 'ya'yansu kar6a66iya ce". "Ai kullum ba ranar banza Inayi miki fa Maryam kedai kawai idan kinje kiyi abinda ya kaiki karki tsaya wasa shine kawai abinda nake so". "Ok shikenan Mama zanyi iya bakin kokarina naga nayi yadda kikace amma please Mama zan roke ki mezai hana ki bari zuwa gobe naje domin kinsan indai abbanmu ya dawo bai sameni ba akwai matsala baya so kayi tafiya baka fad'a masa ba na tabbata indai na tafi bai sani ba zan jawa kaina gaba bazai ta'ba barina na sake zuwa wani gurin ba sai an dau'ki lokaci ne tsawo" jin abinda Maryam tace yasa Mama tai shiru tasan hakan ne gaskiya ta fad'a abbansu mutum ne wanda baison yaronsa ya tafi guri kai tsaye batare daya fad'a masa ba hakan yana matukar jawo fushinsa shiyasa da taji Maryam d'in tace haka itama ta tuna domin zumud'i da saurin da take taga Maryam taje masarautar yasa ta manta da dokar Abban su Maryam d'in................... "Mama bakice komai ba ko kina ganin na tafi ba matsala"? Kai Mama ta girgiza tana cewa "a'a karki tafi kawai ki bari ya dawo ki fad'a masa idan naji ya hanaki nasan abinda zan fad'a masa ya 'kyale kije kawai zance Aunty ce tace kije mata kiyi d'an kwana biyu saboda kin dad'e bakije inda take ba ko ina ganin zaifi yarda akan ki tafi batare daya sani d'in ba maybe a yau idan ya dawo nace kin tafi saiyasa kin dawo kawai mayar da kayanki Allah ya kaimu goben da sauri ba gurin zuwa gara tafiya a hankali maida mu bari ya dawo" to Maryam tace tana juyawa zata mayar da kayan Mama ta bita da kallo a ranta tana sake cewa "insha Allahu Maryam in Allah ya yarda sai kin zama matar Ahmad kwanan nan domin daya amince zai aureki abun bazai dau'ki lokaci ba dan kar wani abuma ya shigo ciki ko akasin da zaisa a fasa" sauke numfashi tai tana samun waje ta zauna tai tsamm tana tunane tunane iri-iri akan yadda zata tafiyar da komai................ HUMM MUJE ZUWA YANZU AKA FARA😁. Washe gari tun safe bayan breakfast zuwa sha biyu Maryam ta had'a kaya bayan Mama ta sake fad'a mata kissa da kisisinar da zata ri'ka yi idan taga Ahmad yana gu da yadda zata ri'ka shishshige masa tana yimasa abubuwan jan hankalin da burga harta samu masauki a zuciyarsa kar tayi sake karta tsaya kallon shashanci tai abinda ya kaita. *** **** Lokaci indai an saka shi me zuwa ya wuce ne su Nadiya an zama amarya a gidan Sabit kamar yadda ake so buri ya cika biki kam anyisa kamar baza'a daina ba an kashe kud'i anyi abubuwan 'karya da son a fad'a a nuna a ranar da za'ai mata rakiya tana zaune a parlon part d'insu tare da 'kawayenta Ayrah ta shigo da sallama d'auke da babban tray a hannunta da kawo musu abinci da abun sha kamar yadda Nadiya ta umarceta tana ajewa kafin ta juya d'ebo sauran wata 'kawar Nadiya ta kalleta tana cewa. "Tofa Nadiya wannan Kuma fa daga ina haka naga ta kawo abinci ba 'yan uwanku bane"? Yatsina fuska Nadiya tai tana had'e rai ta sakarwa Ayrah harara tana cewa "zaki bar nan ko saina tashi na fasa miki idon munafircin ubanki kika tsaya sauraro"? Da sauri Ayrah tabar gurin cikin takaici ta fice da mamaki duk 'kawayen Nadiya suka bita da kallo kafin d'aya tace. "A'a Nadiya ya hakan meyasa kike Mata tsawa kuma"? Tun kafin Nadiya tai magana wataa ta sako baki "nidai banga abinda tai miki ba daga ta kawo abinci sai zagi ita kuma batai kala da 'yar aiki ba balle ace aiki take muku saidai idan bikinki tazo ko"? Kai Nadiya ta girgiza daidai Ayrah ta dawo ta aje musu plate da cokula wani wula'kantaccen kallo Nadiya taiwa mata tana jan tsaki tare da kau dakai kamar irin taga abun 'kyamar nan tace "na tsani wannan yarinyar na tsaneta bana son ko kad'an a dole dama nake zaune tare da ita a gidan nan yau kuma zan bar mata taje ta cinye gidan dama mayya ce taci mutum d'ari da ashirin nidai daga yau na huta da ganin mummunar fuskarta na barwa su Abidah jaraba" dariya Amrah tai tana cewa. "Haba Nadiya irin wannan muzantawa dacin fuska haka wacece ita"?. 'House girl d'in muce man wace bayan meyi mana wanki girki wanke-wanke da share share shine matsayin ta" jin abinda Nadiya ta fad'a yasa cikin takaici Ayrah dake serving d'insu ta d'ago ta kalli Nadiya ba'kin ciki zai kasheta wato itace house girl d'in su lallai d'an adam butulu me manta kyautar jiya............... Har had'a baki sukai suna zaro ido wajen cewa "wannan ce house girl d'in taku kai haba Nadiya fad'i gaskiya dai"?. "Wallahi da gaske nake muku me aikin gidan nan ce komai itace keyi mana muna zaune domin aikin neya dace da ita ba komai ba'' ta karasa maganar tana mayar da kallonta kan Ayrah cikin tsawa tace "ke jaka 6ace min da gani" mi'kewa Ayrah tai kamar zata tanka mata sai kuma ta fasa tana ficewa Amrah da tafi kowa son sanin gaskiya 'kara matsowa kusa tai tana cewa "Nadiya anya abinda kika fad'a haka yake kin fad'a nedai saboda kiji dad'in bakinki"? Murmushi Nadiya tai tana jinjina kai tace "eh a barshi a dad'in bakin ne amma idan Abidah ta shigo ku tambayeta ko bana gurin zata fad'a muku komai zakusan gaskiya nima na fad'a muku yanzun dai kuci abincin nan karya huce dan bata wani iya girki jagwalgwalo take nikam sai ina jin yunwa kamar zan mutu nake cin abinda ta dafa'' ta fad'a tana d'aukar spoon Amrah data riga ta fara ci dariya tai tana cewa "gaskiya Nadiya kiji tsoron Allah ba'a haifi abokin 'karyarki ba ga girki yana tashin kamshi a baki da dad'i amma kici wani idan ba ji kikai yunwa zata kasheki ba baza kici ba"? Tsuka Nadiya tai tana mi'kewa tace "ke kika sani nabar miki aikin nayi gaba" ta fad'a tana fita ta barsu part d'in Hajiya Khubura ta tafi domin ta fad'a tana mata sunyi waya Sabit yace a bata wayar suyi magana bata samu ta kawo mata ba sai yanzu ma ta tuna. Samhat ce zaune tana sauraron wacce ke kusa da ita tana fad'a mata abinda ya faru cewa da gaske ne Sabit yayi aure domin ita Samhat ta 'karyata cewa ba aure zaiyi ba sai yau da labari yazo mata ba iya mutum d'aya ce ta fad'a mata ba mutane da yawa sun kirata a waya sun gulmata mata saboda kowa yasan irin tsananin son da takewa Sabit humm tsabar d'imuwa damuwa tashin hankali da ba'kin ciki da Samhat ta shiga ko gane a inda take bata yi sai duhu da ta fara gani kanta yana sarawa da 'karfi ta mi'ke tana tangad'i da layi tai hanyar fita da sauri Laylah ta tareta tana ri'ko hannunta ta dawo da ita baya a hankali ta zaunar da ita tana cewa. "Samhat kiyi hakuri dan Allah karki fita kina wannan halin ina yanxu kike tunanin zaki tafi" tun Layla bata karasa maganar da take ba Samhat ta sake mi'kewa tana cewa "wallahi bazan yarda ba saina rama saina ba'kanta masa kamar yadda ya ba'kanta min wannan ai tozarci ne tashi ki rakani gurinsa saina 'kaddamar masa da fushina" jin abinda tace yasa Laylah itama ta mi'ke tana cewa "haba Samhat kinsan me kike cewa kuwa me zakiyo a gurin sa inace yasan dake ya barki ya auri wata"?. "Da yasan dani ma sanin ai baiyi min amfani ba nizai yaudara bayan ba fad'a mukai ba sannan tsabar cin mutumci da rainin hankali idan na tambaye shi ance an ganshi da wata budurwar sai yace a'a shi 'karya ake masa babu wacce yake so bayan ni ashe munafirta ta yake yasa duk na rabu da samarin da suke sona da gaskiya sannan zai rabu dani humm yayi da 'yar halak wallahi tallahi tunda yai min haka bazan bari yaji dad'in auren saba saina rabasu saina sanya musu fitina da ba'kin ciki" sosai Laylah ke kallonta jin abinda take cewa tace. "Taya zakiyi hakan bayan aikin gama ya gamu kuma shiba d'an nan bane balle kice iyayensa zaki fad'awa taya zaki rama to"?. "Ta yadda ake ramawar man zan zubar da hawaye na a banza ne wallahi tunda yasa nayi kuka shima sai yayi ai inada numbar wayar mamarsa na ta'ba amsar wayarsa batare daya sani ba nad'au numbar nata da naga yayi Saving da Mah kinsan dana kirata ta tambaye ni wace ni na fad'a mata humn ta ri'ka danna min zagi tana cewa karna kara kula d'anta ita bazata had'a jini da hausawa ba idan na sake kulashi saita hallaka ni to yanxu me kike tunani dayai min wannan butulcin kuma ya auri wata wallahi Laylah saina had'ashi da mahaifiyar shi saina fad'a mata cewa d'anta Sabit yayi aure ya auri bahaushiya ke karshen magana har address d'in inda yake saina fad'a mata tazo taci uwar duk tsinanniyar daya aura". "Yauwa yanzu naji magana kinga ma zaki rama fansar abinda yai miki ta hanya mafi sau'ki kawai hakan zakiyi shine daidai tunda har mahaifiyarsa tace bazata had'a jini da hausawa ba kiyi amfani da wannan damar ki kirata a waya ki fad'a mata harda 'karya ki 'ka'kalo ki fad'a yadda zaki fusata ta sosai ko jirgi ne ta hawo tazo taci ubanta mune 'yan tayayyar duka muyi mata jina-jina domin da biyu xamuyi haka kawai kirata Samhat ki fad'a mata muji me zatace" Laylah na rufe baki Samhat data yarda da duk abinda Laylan ta fad'a waya ta d'auko tana danna kiran numbern mahaifiyar Sabit d'in kiran farko ba'a d'aga ba saida ta sake kira taji an d'auka ana cewa. "Hello". D'auke wayar daga kunnenta tai tana kallon Laylah wacce ta matso tace "ta d'aga fa me zance"? 'kasa da murya Laylah tai tana cewa "ki fad'a mata abinda yake ranki kawai wannan shine ni bansan abinda zakice mata ba ki fad'a mata duk abinda kike so" "ok shikenan bari muga" Samhat ta fad'a tana mayar da wayar kunnenta tai magana jin shiru yasa ta ciro wayar tana kalla ashe an katse kiran kaita jinjina tana sake saka kiran tare da fatan Allah yasa a d'auka tana shiga kuwa aka d'aga ana cewa. "Hello waye ne ya dame ni da kira kuma baiyi magana ba idan baka da abin fad'a ka kashe wayarka"? Kallon juna sukai suna ta'be baki Laylah tace "hum'um wannan matar akwai bala'i keko da wanne tsautsayin ne yaja ki zaki auri d'anta"? Samhat bata saurari abinda Laylah d'in tace ba sai hankalinta data mayar kan maganar da matar take tana cewa. "Ina yini ya gida"?. "Lafiya lou waye yake min magana naga bakuwan number ban santa ba" ta fad'a da muryarta wacce hausa bata wadace taba da yake bayerabiya ce shiru Samhat tai har saida ta sake cewa "nace waye yake magana ko costumer ne me kake son saya"? Kai Samhat ta girgiza tana cewa "a'a ba wani abu zan saya ba nasan baki sanni ba dama na kiraki ne muyi magana akan d'anki Sabit". "Eyy d'ana Sabit kuma meye faru ne wanene ke kike min magana wai d'ana Sabit"? Cije lips Samhat tai tana cewa "dama fad'a miki zanyi Sabit ba karatu yake ba anan da yazo ya gama school da yace zai maimata sheka guda ba gaskiya bane aure yayi" Samhat na rufe baki ta cire wayar da sauri saboda ihun da matar ta saki tana cewa. "Aure kuma Sabit d'in ne ya aure bahausiya ya aura ko kuma waye ya aura fada min gaskiya"? Murmushi Samhat tai jin anzo daidai wajen inda take so matar ta furta wannan maganar tace "kwarai bahaushiya ya aura yau d'in nan aka d'aura auren ko tarewa batai ba shiyasa nace bari na kiraki na fad'a miki dalilin kiran kenan saboda yace bazai dawo Lagos ba sai matarsa ta haihu wai idan kikaga yazo miki da d'a bazaki hanashi zama da bahaushiya ba". "Heyy haka Sabit yace inji ubanwa wallahi ba d'a d'aya ba ko duniya suka haifa saina raba aurensu balle kuma yau aka d'aura auren to bazan bari hakan yaja lokaci ba nagode sose da kika fada min wannan maganar yaron kirki ina godiya zanyi maganin Sabit tunda ya auri bahausen mutum hummm" tana fad'in haka Samhat taji wayarta tace d'it d'it iska Samhat ta furzar tana sau'ke wayar ta kalli Laylah tana cewa. "Yauwa alhamdulillahi sai yanzu naji dad'i dana rama gaskiya Laylah kin iya kawo kyakkyawar shawara na tabbata tunda har mahaifiyarsa taji wannan labarin tofa 'karyar duk shegiyar daya aura ya 'kare ko tana so ko bata so zata zama bazawarar dole shi kuma taci 'kaniyarsa humm Allah yasa kafin ta rabasu saita nunawa tsinanniyar daya aura jikinta da duka" dariya Laylah tai tana kallon Samhat wacce ta karasa maganar harda d'aga hannu sama alamar Allah ya amsa mata tace "kina burge ni 'kawar shiyasa nake yinki to yanxu dai kin rama dan haka saiki saki jikinki mu sha'kata tunda kema yanzu kina da wanda yake sonki dan kin 'ki amince masa ne amma nasan zaki kar'bi gayyatarsa bayan da wannan al'amarin ya faru ko"? Shiru Samhat tai kamar me tunani tai tsam sai can ta d'aga kai tana cewa "eh yanzu kam na amince zan iya soyayya dashi idan ta kama har aurensa nayi nifa dama tunda na kira wannan mahaifiyar Sabit d'in a wancan lokacin ta zageni tas ta ri'ka aiko min da ashar tai min barazar zata kasheni idan ban rabu dashi ba tun sannan nayi tunanin rabuwa dashi sai kuma naji bazan iya ba sai gashi ya raba ala'kar mu da kansa hakan yayi min dad'i sosai ya bani citta" dariya Laylah tai tana cewa "indai ya baki citta har haka to tashi mu tafi mu d'ebi nishad'i ki manta da wannan gayen kisa a ranki kamar baki ta'ba saninsa ba" mi'kewa Samhat tai tana cewa "a shirye nake muje kawai" handbag da key Laylah ta d'auka suna fita daga bedroom d'in da suke suna tafe tana sake bata shawarwari akan yadda zata fara soyayya da wannan sabon saurayin nata. Tunda Mah suka gama waya da Samhat ta mi'ke tana zaga parlonta ranta a 'bace ta kira numbern Sabit bai d'aga ba qara kiransa tai nan ma no answer kaita jinjina tana zama ta zubawa secreen d'in wayar nata ido iya kallon numbern Sabit da take ranta qara 'kuna yake zuciyarta tana tafasa wuce numbar tai ta kira wata dabam wacce bugu d'aya aka d'aga ana cirawa tace "hello Boukar kazo yanxu ina son ganinka" ta fad'a tana aje wayar da kamar minti sha biyar wani saurayi ya shigo yana zama yace. "Barka da gida Mah meya faru naga kamar ranki a 6ace yake"?. "Eh raina a 6ace yake man Boukar ni Sabit zai mayar mahaukaciya na fada masa bana so ya auri hausa women amma tsabar na zama uwar banza ashe yace min ya koma karatun shekara guda zai maimata yaje yayi aure yau d'in nan ya auri bahausiya humn kasan me nake bu'kata so nake ka shirya ka tafi can ka gane min da gaske Sabit aure yayi ko 'karya ne domin wacce ta kirani ta fada min bansanta ba kawai naga ta kirani ne". Kaiya d'aga yana cewa "ok Mah ba matsala zanje zan gano miki komai kuma zanyi kokari naga na 6oye masa yadda bazai san ina garin ba harsai na gano miki komai saina kiraki na fad'a miki". "Ok Boukar nagode idan ka shirya kayi min magana na baka kud'in mota kaje duk ma inda yake ka gano min walay sai naci uban Sabit zaisan yaje yayi aure batare da neman izini naba" mi'kewa Boukar yayi yana mata salama ya fita da shirin gobe da safe zaizo su karasa magana ya kar'bi kud'in mota ya taho neman Sabit d'in yabar Mah ranta a 'bace jiran dawowar su Niseh take daga school ta fad'a musu..............✍️Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë. TYPING 📲 +234 816 098 30 83 WhatsApp number chat with me at always my lover's ina maraba da kowa. 👑 ROYALTY 👑 💫 A*W*A 💫 ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫 Home of hospitality and harmony gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan ta haka taken mu yake tafiyar babu rago babu maci amana tsantsan gaskiya muke nunawa. STORY WRITTEN ND EDITING ✍️Yusrah Musa Abubakar YUSEEN AL-AMEEN CE maman Fatima Zarah Elham little Zarahn Aunty. 11~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Sajidinah. @YUSRAHMS CE Page 21 & 22 👑 Empire 👑 Kwanan Maryam biyu da zuwa masarauta Baby batasan da zuwanta ba saboda sa6ani suke lokacin da zata shigo Maryam tana bedroom ko kuma Babyn tana fita Maryam d'in zata fito basu ta'ba had'uwa ba babu wanda yasan wani a cikinsu Khairat kuma bata fad'awa Babyn sunyi ba'kuwa ba kawai dai taga kwana biyun duka a part d'in Mami suke kwana sai yanzu data shigo taga Maryam a zaune ta hakimce sai sham 'kamshin take da waya a hannunta ta d'ora 'kafa d'aya kan d'aya ko d'agowa batai shigowa Baby tai da sallama tana zama iya Khairat ce ta amsa mata tana kallonta tace "daga ina haka"?. "Part d'in Mami man fatan ya Ahmad baya part d'in nan"?. "Ban sani ba nima fitowa ta kenan amma da alama dai baya nan domin idan ya shigo baya wuce parlor" gyara zama Baby tai tana sau'ke ajiyar zuciya tace "yauwa masha Allah bari na bararraje nasha iska kafin ya shigo na fece boss me zamani namu" jin abinda tace yasa Maryam ta d'ago kanta kad'an tai mata wani d'an iskan kallon qasan ido a ranta tana cewa "wannan kuma fa itama kenan a gidan take kodai 'yar gidan 'kanin Abbansu Khairat ce"? Ta'be baki tai tana d'auke kai duk da bata gaji da kallon nata ba ta mayar da hankalinta kan abinda take a waya iya Khairat da Baby ne suke magana a gurin harda dariyarsu saboda sun san Ahmad baya nan tsaki Maryam taja irin sun takura mata d'in nan saidai batai musu magana ba kallon Khairat Baby tai cikin basarwa kamar da bataga maryam d'in ba sai yanzu tace. "Aunty Khairat ba'kuwa kukai ne yaushe tazo"?. "Eh ba'kuwa mukai 'yar gidan 'kanwar Momy ce sunanta Maryam" kai Baby ta d'aga tana cewa "sannu da zuwa Aunty Maryam ya kike fatan kinzo lafiya"? Cikin yau'ki da yanga Maryam ta yamutsa fuska kamar bazata amsa ba cikin nuna ita watace. "Kalau kefa"?. Banza Baby tai mata dan ta tsani rainin hankali ta zage tai mata magana amma ita ta bata wannan jakar amsar ta'be baki Maryam tai tana jan tsaki ta kalli Khairat tana nuna Baby da yatsa tace "Khairat wannan kuma wace ita"? Hankalin Khairat nakan waya batare data daina abinda take ba tace "Zuhra cefa 'yar gidan Abba Ashraf cousin d'in muce muna kiranta Baby wani lokacin kuma ya Ahmad yana cemata little" dariya Maryam tai cikin rainin wayo tace. "Lallai kam naga little anan sai kace 'kwaro nifa saida kikace haka na tuna yarinyar nan tabbas na ganeta yanxu a sunanta ne muka sha minti muka ci ragon suna right"? Ta fad'a tana kallon Baby tun kafin Khairat tai magana Baby tace "a'a kin manta ashe ba kece kika haifeni ba"? Tafi Maryam tai tana murza yatsunta suka bada sautin 'kas 'kas tana d'age gira tace. "Hummm yarinya kenan kusa dagun dan wallahi a haihuwar kaji ke tatta6a kunne nace" ta karasa maganar tana doka mata harara d'aga mata hannu Baby tai ranta a 'bace tace "enough is enough malama Maryam ya isheki haka ki tsaya iya matsayinki bana son harkar 'karanta". "Hum little kenan 'yan mata ni kuma ina son harkar 'karanta saiya"?. "Karki sake ce min little". "Idan na sake fad'a fa zaki dakeni ko zaki d'au mataki dan naga kin fusata da yawa ke a tunanin ki zaki iya yimin wani abune"?. "Kwarai ba abu guda d'aya ba zan iya yin abubuwada yawa idan tsautsayi yasa kika sake kira na little saina baki mamaki wanda har ki mutu baza ki manta dani ba" Baby tana rufe baki Maryam ta fara dariya kamar zararriya tana nuna Baby da yatsa juyi Ahmed keyi tare da toshe kunnensa domin yana can a cikin wasu manyan kujeru dake gefen farlon suma anyi musu kwalliya an tsara guri ba wanda yasan dashi domin tunda ya shigo gurin ya zarce ya kwanta a d'aya daga cikin kujerun barci ya d'auke shi dariyar maryam ce ta tadashi tsuka yaja da qarfi jin abin bana 'kare bane ya tashi zaune yana mikewa yaga waye wannan shashashan ba Baby ba hatta Khairat taji haushin abinda Maryam din keyi fitowar Ahmad daga gurin round kujerun da yake kenan ganin Maryam ce dama yasan saidai ita Baby ko Khairat baza suyi wannan d'abi'ar ba ko baya nan balle sunsan yana gari tsayawa yai ransa a mugun 'bace ya buga mata tsawa mai 'karfi wacce tasa tai shiru tana kallonsa ta kafeshi sosai da ido domin batasan yana part d'in ba muryarsa da fushi yace. "Wanne irin hauka ne wannan amfad'a miki nan irin gidanku ne da zaki ri'ka yiwa mutane hayaniya da ihu karki kuskura na sake jin kinyi koda tari ne wanda bai gamshe niba wallahi saikin gwammace baki zo duniya ba yau idan bakisan waye niba ko kin manta waye ni ki tambayesu su fad'a miki" yana fad'in haka ya juya da kallo maryan ta bishi tana ta'be baki ta kalli su Khairat wadanda suka shiga taitayinsu tace "ok fatan kunji abinda yayan naku yace saiki bani amsa bansan waye shiba a cikin ku wace zata fad'a min shid'in waye"? Daga Khairat har Babyn kowa banza tai mata babu wacce ta qarasa kallonta balle tasa ran zasu bata amsa tsaki taja tana cewa. "Humm matsala ta daku duk haka kuke jininku d'aya izzarku d'aya 'ya'yan masarauta akwai girman kai wato tambayar danai ma an rasa me bani amsa a cikin ku bayan shi yace na tambaye ku"?. "Me kike so ki sani"? Khairat ta tambaye ta domin Baby ta d'auke kanta ko kallo bata isheta ba kai Maryam ta jinjina tana kallon Khairat cike da neman fitina tace "ba kece zaki bani amsa ba gada wacce nakeyi can ai tafi nuna ita jinin sarauta ce irin izza da jin kan Ahmad gareta ko daga iya kalamanta sai kace wanda bakinsu a had'e koke da kuke uwa d'aya uba d'aya baki d'auko kamarsa halinsa da d'abiunsa kamar yadda wannan Babyn ta d'auko ba kalli man hatta fuskarsu iri d'aya ne me hakan yake nufi ba cousin d'inku bace"?. Kallon Baby khairat tai tasan abinda Maryam ta fad'a gaskiya ne baby suna kama sosai da Ahmad amma ina ruwanta da yawan shishshigi dason shiga safgar da ba'a saka da ita ba wannan fa yada girma ne da yace ta tambaye su indai ba neman magana ba mene na cewa Baby ce zata bata amsa mayar da hankalinta kan Maryam d'in tai jin tace. "Ina sauraronki fad'a min waye shi ina so na sani dan ban sanshi ba fad'i man"? Ko inda take Baby bata kalla ba kuma bata nuna alamar tana jin abinda ta fad'a ba balle tace zata bud'e baki ta bata amsa sai kokarin mi'kewa da take zata bar gurin Maryam tace "madam ji mana babu fa inda zan barki kije saikin fad'a min waye shi saboda yace na tambaya so nake nasan waye shid'in kin gane"? Batare da Baby ta kalli inda take ba tace. "Aike baki isa ki sani abinda banyi niyya ba saboda bada kowa nake iya magana ba tsabar izza da jin mulki kinsan mu jikanun sarki jinin sarauta 'ya'yan sarakai tashin 'kasaita dole saida sham 'kamshi ba daga anyi mana magana muke mayar da martani ba sai an dau'ki dogon lokaci idan zaki iya jirana fatan kin gane yanzu domin da Baby kike magana bada little ba" ta fad'a tana watsa mata wani irin kallo wanda indai ba zigo idon Maryam yake mata ba irin kallon da Ahmad yake mata ne a duk lokacin datai masa magana humm iya hakan yasa taji ta tsani Baby ko ganinta yanzu haka bata son yi" kaita jinjina tana cewa. "Humm lallai yarinya kin taro abinda yafi karfin ki ni nan da kika ganni" Maryam ta fad'a tana nuna kanta taci gaba "niba sa'ar raininki bace karkiga nazo gidanku ki nemi fad'a min magana ko kice zaki abinda bai gamsar dani ba wallahi saina gwada miki yadda ake rashin mutunci domin niba kanwar lasa bace zafina yafi barkono ki bini a sannu ki huta dan na tambaye ki baki isa ki nuna min izza ba babu ruwana da wace ke zan rufe idone nayi miki kaca-kaca na wulakanta ki kuma na zauna lafiya idan kina ganin abinda na fad'a 'karya ne to kici gaba da raina min hankali zanyi maganinki" ta karasa maganar tana sakar mata mugun kallo taja tsaki tana gyara zama numfashinta har sama yake saboda yadda tad'au zafi akan abinda Ahmad ya fad'a mata da kuma abinda Babyn ta fad'a mata murmushi Baby tai ganin ta fusata ta jinjina kai tana mi'kewa cikin son sake d'ora mata hau ta wuce dinning ta ciko plate da abinci tana dawowa ta aje a gaban Maryam wacce ke binta da kallo sannan ta koma ta qara ciko wani ta d'auko mata robar ruwa duk ta aje mata d'agowa tai har lokacin da murmushi akan fuskarta gira ta d'age alamar yadai ganin Maryam d'in tana kallonta kafin ta fara magana. "Haba goaty🐐 duk wannan shariyar danai bai isheki ba sai kin nuna halinki to gashi nan na kawo miki dusa sai kiyita fama nikam bana cacar baki da wanda baisan me yake ba fatan kema kin gane me nake nufi? Sannan zan gargad'eki ko a gaba kada kuskure yasa ki sake fad'a min wani abu wanda kaina bazai dau'ki rainin kiba zan iyayin abinda bakya tunani dan haka respect your self wannan shine gargad'i na a kanki nafarko kuma na qarshe idan kika sake shiga hurumin da ba naki ba a kaina zakiga matakin dazan d'auka domin bani naje inda kike ba kece kika zo har gida kika sameni tsautsayi da asara ne zaisa ki sake min hauka a gidan nan kafin ki tafi zan nuna miki iyakar rashin mutunci kuma zaki gani" tana fad'in haka ta juya tana ficewa daga part d'in gabadaya ta koma part d'in Mami. Cikin takaici Maryam data bi kofar da Baby ta fice da kallo ashra ta saki tana cewa amma sai naci bura uban............... Da sauri Khairat ta rufe mata baki tana girgiza kai tace "please Maryam dan Allah karki 'karasa kar kiyi mana ashar anan domin ba'a yi karki fara dan Allah koma mene kece kika fara ta'bo ta" bige mata hannu maryan tai tana cewa "oh da baki magana ba lokacin da take min rashin kunya saboda kina tsoronta sai yanzu dan zan zageta kike kokarin hanani saboda ki nuna min matsayina ta fini daraja a gunki. Kai Khairat ta girgiza tana kallon yadda Maryam ta fusata tace "A'a ba haka bane ya kamata ki fahimta karkiwa abun gurguwar fahimta ni bance miki haka ba karki fassara hakan da wata manufa dake da ita duk d'aya na d'aukeku kowa jini nane bana bambanta ku". Wani irin kallo Maryam tai mata a she'ke tace "kikace dani da ita duk d'aya kika d'auke mu duk d'aya fa? a hakan amma ta zageni baki hanata ba saini na tashi zaginta ki hana kuma tsabar kin goge min hadda kice wai d'aya muke? Lallai Khairat kina da abun mamaki to wallahi bari kiji bazan ta'ba 'kyale yarinyar nan ba saina nuna mata kura ba farkar kare bace". "Um um kinga Maryam karki tadawa mutane hankali a gidan nan ya Ahmad yana nan ki jawo mana wahala idan ke bazai dake kiba mufa ba irinki bane gaskiya karki wannan maganar ko ki maimaita idan Momy ta fito nidai ba ruwana bazaki jawo mana bala'i muna zaune lafiya ba". Tsaki Maryam taja me qarfi tana cewa "saime dan kince ba ruwanki dama nace ki ruwane ko kina da ruwan ma me zanyi dashi ni zanyi kayana nice zanyi maganin abun kuma ba duka ba ko kasheku Ahmad zaiyi a gidan nan sai nayi wannan maganar Allah ya fito da Momyn lafiya ke bari kiji karshen rashin mutunci bazan fad'a bama sai naga ya shigo sannan na nuna irin cin fuska da zagin datai min har iyaye na da kakanu na saida ta kira ta zaga kuma tace min akuya haka zance inyaso ya dau'ki ranta a take a kaita ma'kabarta meye damuwata da hakan"?. Kai Khairat ta kad'a tana cewa "ok shikenan kiyi abinda kikaga dama tunda ba'a fad'a miki gaskiya ki d'auka nidai nayi iya yina abinda ya kamata nake fad'a miki matsayin ki na 'yar uwa gareni badan dai kin yiwa abin gurguwar fahimta ba kince na za'bi Baby a kanki amma fa maganar gaskiya ba haka bane kawai wannan zatonki ne keda ita duk d'aya kuke a wajena anan ina kokarin fad'a miki gaskiya ne". Khairat na rufe baki a masife Maryam tace "gaskiyar ki d'in banza a hakan kike fad'a min gaskiya kina goyon bayanta tana qanwar qanwata ta zageni saboda rashin kunya ko kema kinsan keba sa'ata bace na fiki balle ita dan tayi tsayin 'kafa taga kafad'arta tazo daidai da tawa shiyasa xata raina min hankali to wallahi bata isa ba tayi kad'an ita d'in banza zatasan wace ni sai naci uwarta a gidan nan kafin na tafi". Mi'kewa Khairat tai tana cewa "shikenan Maryam bari na baki gurin kici gaba dayi amma banga amfani ina fad'a abinda ya kamata kiyi ke kuma kina watsarwa ba gara na baki fili kiyi komai lokacin kine saboda kome zakiyi ya Ahmad bazai kulaki ba mu kuwafa duka zaki jawo mana sannan Dan kin maimaita magana a gabansa ma da kike cewa zaki fad'a idan naji ba gaskiya kika fad'a ba zanyiwa ya Ahmad bayani domin bazan bari ki jawowa Baby duka ba tunda ba itace ta fara tanka kiba kece kika shiga abinda babu ruwanki" tana fad'in haka tai waje tabi bayan baby xuwa part d'in Mami a bedroom d'insu na part d'in ta sameta tana zaune ta shiga tana zama ta fuskanceta sosai saboda ita kanta yanzu haushin Maryam ya kamata balle Babyn da sukai hakan da ita kallonta baby tai tana cewa "Aunty Khairat ya kika baro ba'kuwar ita kad'ai kuma kika taho nan"? Kai Khairat ta girgiza ranta babu dad'i tace. "Dan Allah Baby kiyi ha'kuri kinji"? Da mamaki Baby tace "ha'kurin me kike bani kuma"?. "Ha'kurin abinda ya faru yanzu kar kisa abun a ranki na sani maryam bata kyauta ba amma na wakilce ta nabaki ha'kuri sannan karki bari abun ya ri'ka damunki" kai Baby ta girgiza tana murmushi tace "aini Aunty Khairat bana ri'ko a take na manta da wannan shafin bansa aka bama balle ya dameni badan yanxu kin tada zancen ba nifa harna manta kamar komai bai faru ba haka nake jina kuma ko yanzu na koma zan iya gaisawa da ita wannan ba komai bane". "Humm na sani Baby amma ni ban manta ba saboda abinda tai miki was in proper sam bai kamata ba babu tsari a ciki wallahi ba 'karya ko ganin idonki ba Baby naji kunyar abubuwan data fad'a miki domin bai kamata ba". "To aunty Khairat mene abun jin kunya wacce tai abun bai dameta ba saike sannan sanin ya kamata Ita a ganinta ya kamata d'in tunda abinda ke ranta ta fad'a komai da kikaji ya fito gaskiya tai bata 6oye ba balle ya dameta saboda ya Ahmad yai mata magana ne ta nemi huce haushinta a kaina ba komai ba shiyasa ma abun ko d'ara ni baiyi ba kuma koba haka ba itama 'yar uwarki ce ta jini sosai". "Kuma amma idan ita 'yar uwata ce karta manta kema hakan kike ba zaman gida d'aya ne ya had'a mu ba mahaifanmu uwarsu daya ubansu d'aya kakanin mu d'aya kamar yadda itama ta nata 6angaren haka abun yake to mene abun d'aga harshe da fitina anan indai ba neman kar a zauna lafiya ba"?. "Hummm Aunty Khairat itafa takaicin ta dan kawai yace ta tambaye mu sai haushin abun ya dawo kaina saboda muna kama dashi kamar nice nasa shi yazo yai mata magana balle tace tsanarta nayi ni ban ta'ba ganinta ba sai yau kuma daga had'uwa maimakon a sha'ku ayi zumunci saidai fad'a da fad'ar maganganu ya biyo baya gaskiya Aunty Khairat bazan 6oye miki ba abinda ta fad'a ya 6ata min rai amma tun d'azu yanxu kam ya dad'e da wucewa na manta da shafin kema ki manta kawai muyi abinda ya dace". Cikin jin dad'i Khairat tace can"ok Baby shikenan nagode da kika fahimce ni kumà kika fahimce ta amma ita ta kasa fahimtarki nayi iya yina ta gane inda kika dosa ta'ki amma ke sabida akwai fahimta me karfi a tsakanin mu gashi kin fahimci inda maganata ta dosa tun wuri ba komai zanyiwa Momy magana bari a jima". "A'a Aunty Khairat please dan Allah karki fad'awa Momy komai ki 'kyale ya wuce koda ace itace ta taso da maganar karki tanka na ro'keki wannan alfarmar" ta fad'a tana had'a hunnunta"? Kai Khairat ta d'aga tana cewa "ok tom shikenan Baby bazan fad'a ba ya wuce d'in kamar yadda kika ce Allah ya sauwa'ke" Amin kawai shine abinda Baby tace tana d'aukar littafin da take karantawa taci gaba Khairat kuma ta karasa hawa gadon tana kwanciya tace "bari mu d'an matse barcin minti talatiin kafin lokacin islamiyya yayi mu tafi" d'agowa Baby tai tana kallon yadda tai baje-baje kawai dariya tai tana cewa "tabd'i Aunty Khairat kinsan mena hango ace yanxu barci na dau'ki ki ya Ahmad ya shigo bedroom d'in nan" ta karasa maganar tana sake sakin wata dariyar ganin yadda Khairat ta zaro ido waje tana cewa "Kai amma gaskiya baby kin iya salon mugunta humm insha Allahu har nayi barcina na tashi bazai nemi inda muke ba ai naga kwana biyun nan ya daina kulamu tun ranar dayasa mu watering d'in nan muka fara samun hutu maybe Momy ce tai masa fad'a" jinjina kai Baby tai tana cewa "ta yuwu hakan ne tunda ita tasan abinda ya faru". "Ke hakan nema shiyasa yad'an bamu guri mu sarara wallahi kinsan dan ra'ayin kansa bazai d'aga mana qafa ba ya Ahmad humm bakai laifi bama nema yake ya d'ora maka danya dake ka balle ya kamaka da lefin dumu-dumu mudai gamu ga Allah shine kad'ai me ceton mu" Khairat ta fad'a tana sake gyara kwanciya tare da rufe ido murmushi Baby tai tana girgiza kai batai magana taci gaba da karatun da takeyi amma ita kad'ai sai murmusawa take saboda wani lokacin idan ta tuna cewa Ahmad ko bakai masa lefi ba zai nemi d'an wani abun damuwa ya d'ora maka dan kawai ya dake ka ko ya saka punishment dariya ta saki tana aje littafin itama ta kwanta a kusa da Khairat................✍️Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë 🌺. See you tomorrow morning. Tnks for ur supports 🔥. Be with me at always my lover's. TYPING 📲 Mon April/2025 8:56am YUSRAH 🤞 MUSA 🤞 ABUBAKAR 👑 ROYALTY 👑 💫A*W*A💫 Home of hospitality and harmony ANNURI haske daga Allah marubuta masu hazaka hikima da sanin ya kamata masu cike da baiwa da basira mahankalta ma'abota iya magana da sarrafa harshe. ____________________ _____________________________ _____________________________________ In the name of Allah the must benefits and the must merciful ALLAH THE MOST HIGH DOESN'T SLEEP ALLAH THE MOST HIGH IS PURE HE ACCEPT ONLY WHAT IS PURE. Manzon Allah SAW May the blessings and the peace of Allah be upon you ya rasulullah muna sonka fiye darai da iyaye da dukiya no success with you, you the light of every darkness you have no limits. 12~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Qaiminah. Bismilllahir Rahmanur Rahim 📿 @YUSRAHMS CE Page 23 & 24 Maryam tana ta dakon dawowarsu part d'in ta shirya bala'i iri-iri amma shiru har dare taga basu sake le'kowa ta ciji yatsa ta qara kamar zata fasa ihu haka take jin takaici ji take a ranta inama zata iya dawo da d'azu da babu abinda zai hana taiwa Baby mugun dukan halaka wanda koda a gaba akace tai mata kallon banza bazatai ba amma hakan ma ba ha'kura tai ba tana nan da ita ta kasa ta tsare jira take ta shigo part d'in kawai ta dam'ki wuyanta ta matseta sai taga ta kusa mutuwa numfashinta yana shirin fita kodama ace zata barta ganin ba dawowa zasuyi ba gashi kusan qarfe tara da rabi tayi harta kwanta ta mi'ke tana d'auko hijab d'inta ta fito tayi sa'a kuwa Ahmad yana gurin Momy wani irin daddad'an numfashi ta sauke da sauri ta karasa tana zama ta sauya fuska ba walwala muryarta da yanayin damuwa kamar zatai kuka tace. "Momy ina yini"? Kallonta Momy tai sosai ganin yanayin ta da yadda take sunkuyar dakai yasa ta fahimci akwai abinda take so amsa mata tai tana cewa "Maryam lafiya kuwa naganki a haka kamar bakya jin dad'i ina su Khairat d'in ko har sunyi barci ne saike kad'ai suka bari"? Kaita girgiza kuma ta'ki ta d'ago ta kalli Momyn dan karta gane cewa abinda zata fad'a mata 'karya ne............. "Ina jinki Maryam meya faru"?. Kukan 'karya ta fashe dashi tana goge ido kamar gaske tace "Momy me nayiwa Khairat ina matsayin 'yar uwarta amma dan nazo gidan nan kamar wacce a kanta nake xaune tun ranar da nazo ta sauya min fuska babu maganar arzikin da zata shiga tsakanin mu sannan ta daina kwana a part d'in nan bansan inda suka koma da kwana ba ni kad'ai nake kwanciya kamar wata mayya ban Isa nayi wargi a cikin su ba sun had'e min kai ita da wannan yarinyar Baby gaskiyar ban ta'ba tunanin hakan daga Khairat ba da wani ne yace idan nazo zata wula'kanta ni bazan yarda ba saida na gani da idona wai d'an uwanka ya ri'ka ma kallon banza sabida kazo gurin sa" ta karasa maganar tana sake fashewa da sabon kukan 'karyar da take yi Momy data zuba mata ido tana kallon ta kuma tana sauraron abinda take cewa har takai aya daga ji tasan wannan ba gaskiya bace had'i ne kawai irin na Maryam Khairat bazata ta'ba yi mata wani abun rashin dad'i ba amma saboda kar tace ta baiwa 'yarta gaskiya ita kuma ta bata rashin gaskiya tunda d'an Adam ba'a iya masa sai tace. "Subahanallahi Khairat d'in ce meyin duk wadannan abubuwan batare dana sani ba meye ya had'aku da farko ai naga lokacin da kika zo tana ta murna sai hira kuke kuna dariya cikin nishad'i amma ko sati baki ba har kunyi fad'a yanzu ina ita Khairat d'in take"?. "Ni bansan inda tai ba tunda suka fita ban sake ganin ta dawo ba wai sunbar min part d'in na dafa na cinye tunda na gaji maita". "A'a subahanallahi baki gaji maita ba sannan bazaki dafa ki cinye ba sunyi hauka ai ba'ko mutum ne me girma da karamci wanda zaka karrama shi kake nan nan dashi amma su sai suke miki irin haka? Kiyi hakuri zanyi musu fad'a gobe idan Allah ya tashe mu lafiya zan sa6a musu indai sun tabbatar min cewa hakane abinda kika fad'a". Ko kunya babu Maryam tace "wallahi hakane gaskiya na fad'a miki Momy kamar ni ace wannan yarinyar Zuhra take kowa sunan nata bai dameni ba? Humm wai akan Ahmad yace na tambaye su waye shi d'azu bayan ya tafi na tambaye su ta hau yimin rashin kunya tana zagina tsinuwa iri iri da ashar kamar wacce nayi wani abun muniya daga tambaya wai kuma a hakan har fad'a take waisu 'ya'yan sarakuna ne jikanun sarki da sarauniya ba'a ta'ba su a wanye tafiya izza da girman kai a jininsu take". Baki bud'e Momy kebin Maryam da kallo yanzu kam tasan 'karya take Baby bazata ta'ba yin wannan abinda ta lissafa ba domin ba irin tarbiyyar da aka koya musu ba kenan "Babyn ce ta zageki sannan ta fad'a miki dukkan wadannan maganganun marasa dad'in ji"?. "Kwarai itace Momy ai zagin datai min bazan iya maimaitawa ba saboda muninsa taci mutuncina sosai d'azun nan ta wulakanta ni fiye da kima gaskiya Momy kiyi mata fad'a haba yarinyar nan kamar mara nutsuwa haka take abinda taga dama bayan ta qare min zagi harda cewa tasan karshe dawa zan had'ata bazai wuce Ahmad ba kuma shima ba tsoronsa take ba kawai dai tana d'aga min qafa ne da taga ni ba'kuwa ce kiji fa Momy idan ba rashin kunya ba Ahmad ba yayanta bane? Amma cewa tai shima yayi kad'an yace zaiyi mata wani abu ko yad'au mataki a kanta zagin datai min kuma ta zagi banza ba wanda ya isa tararta da wata jakar magana akan abinda tai min". Kai Momy ta girgiza tana sakin murmushin da bata shirya ba domin wannan wasan 'kwai'kwayon da Maryam ta shirya batai nasara ba ko Ahmad baya duniya qarewarta kenan ta tabbata Baby bazata ce bata tsoronsa ba ko tace babu wanda ya isa ya hukunta ta balle tasan yana cikin gidan hum ta fahimci ba zaman lafiya ya kawo Maryam gidan ba babu wata ziyara da tazo musu kawai tazo d'aga musu hankali ne dole zata dakatar da ita dan bazai yuwu ta ri'ka shiryo 'karya tana zuwa tana karanta musu ba dan ta zama gizo................................. Katse mata tunani Maryam tai ta hanyar cewa "kuma abun ba'kin cikin ma harda Khairat itace me taya ta tana zugata ta wulakanta ni wai nazo musu gida zanyi kwad'ayi ina gidan ubana da bazan zauna ba ko baza'a iya ri'ke ba shiyasa ta tattaro na dawo musu nazo ina addabarsu to suna daidai dani idan ban had'a tsunmokara na nabar gidan nan ba wata rana sai sun yimin dukan dazan kasa tash.................. Bata karasa ba Momy tace "kinga Maryam kiyi shiru haka ya isa dan Allah bana son sake jin komai indai su Khairat ne kiyi hakuri zanyi magana dasu tashi ki tafi ki kwanta Allah ya tashe mu lafiya" shiru Maryam tai zuciyarta babu dad'i wanda tazo tana yin maganar danya tanka harta gama ko kallon inda take baiyi ba balle tasa ran zaice wani abu zazzafan huci ta fitar tana mi'kewa kamar zata rufe Momy da duka akan tafiya ta kwanta d'in da tace tayi da'kyar ta mi'ke tana turo baki tace "saida safe" ko jiran amsar da Momyn zata bata batai ba fuuuu ta wuce tana bud'e kofa ta shiga tana rufowa da qarfi kai Momy ta jinjina tana bin kofar da kallo zatai magana Ahmad da yaja tsaki yace. "Momy zaman me take banga amfanin zuwanta ba tunda tazo gidan nan take had'a fitina da damuwa a tsakanin yaran nan suna zaune lafiya haka kawai ta baro gidansu taxo ta d'aga musu hankali to wallahi bata isa ba ki fad'a mata sa'ko daga ni ta had'a kayanta ta koma gidansu idan ta'ki zataga sakamakon taurin kai zan nuna mata niba sa'an wasan ta bane tsabar ta rainawa mutane hankali Babyn ce zata iya fad'ar duk wadannan stupid d'in maganganun data lissafa ai daga nan zaki fahimci zama tai ta shirya kayanta nasan halin 'kannai na nasan abinda zasu iya da wanda bazasu iya ba dan haka ki fad'a mata tayi taka tsantsan karta kuskura na sake jin bakinta ya shirya wasu banzayen kalamai sannan ta jigina su tace Wai Khairat da Baby ne suka fad'a idan ta sake ranar zata ga 6acin raina dan zan nuna mata tayi kuskure". Sauke ajiyar zuciya Momy tai tana cewa "gaskiya ne Ahmad dukkan zancen nan da Maryam ta fad'a babu 'kamshin gaskiya a ciki kawai dai na biye mata ne kartaga kamar ina goyon bayan su wulakanta tane nikuma duk d'aya suke a gurina bana bambanta su itace take kokarin saita fahimci a wanne irin muhalli na ajeta". "Ok abinda take son sani kenan? Ta samu zan sanar da ita Allah yasa na sake jin ta maimaita hauka irin wanda tai yanzu na rantse da Allah ranar saita kwana da tsattsaman jiki babu ruwana da girmanta indai tai abinda ba daidai ba saina hukunta ta kamar yadda nake hukunta su Khairat" yana fad'in haka ya mi'ke yana shirin fita yace "goodnight Mom ki huta lafiya"? "Ok Ahmad Allah ya kaimu saida safe" yana fita Momy ta mi'ke taje ta saka lock a kofar kafin ta dawo ta wuce part d'inta Maryam dake la6e tana jin komai hawayen ba'kin ciki ne ya zubo mata ba maganar da Ahmad yayi ne ta 6ata mata rai ba a'a ganin datai har lokacin bata fara samun lambar yabo wacce xata samu shiga a gurinsa ba shine ya sakata kuka ashe dama duk wankan da take d'auka da kwalliyar da take yi baya gani a banza takeyi ko kallo bata ishesa ba balle ta fara kokarin jawo hankalin sa sakin kofar tai tana kuka taje ta d'au wayarta a daren karfe sha d'aya tayi amma bata lura da wani lokaci ba saboda tashin hankalin da yake gabanta Mama take kira burinta kawai ta d'aga suyi magana Kota samu salama. Mama tana kwance a bedroom Abban su Maryam shi kuma yana gaban laptop yana rage aiki yaji wayarta na ringtone da mamaki ya kalli Mama da ke sharar barci kamar ya tashi ya duba waye me kira a wannan daren sai kuma ya fasa ya mayar da hankalinsa kan aikinsa jin an sake kira yasa yai tsaki yana tashi yaje har inda take kwance ya tasheta cikin magagi Mama ta bud'e ido tana cewa "Alhaji lafiya kake tashi na" batare daya bata amsa ba ya juya yana komawa inda yake da mamaki ta tashi zaune tana kallonsa zatai kira na uku ya shigo zaro ido waje tai cike da fargabar waye yake kiranta a wannan daren kodai akan haka Abba yai fushi da sauri ta dau'ki wayar tana kallon number Maryam jikinta na 6ari ta kasa d'agawa har kiran ya katse kallonta sosai Abba yai yana cewa "Waye yake kiran wayarki a wannan daren"? Kai Mama ta girgiza cike da tsoro muryarta nadan rawa tace "Maryam ce" jin abinda tace yasa baida niyyar d'agowa amma saida ya daina abinda yake yi ya kalleta kamar bazai tanka ba sai kuma. "Maryam dai me zatai miki a wannan daren nifa irin haka ne bana so hankalina bai kwana da yarona yaje wani guri har yayi kwanaki ba kawai dai na barta ne saboda naga gurin yayarki zataje amma badan haka ba wallahi babu inda ta isa taje a wannan yanayin da ake ciki tana mace bana so ta ri'ka nisa da gida" shiru Mama tai tana rarraba ido ta kasa magana sai numfashi da take saukewa kamar wacce tai gudu ganin duk tabi tayi tsuru-tsuru yasa yad'an girgiza kai yana mayar da hankalinsa kan aikinsa bai sake ce mata komai ba Mama da jikinta ya gama sanyi so take tayi masa bayanin abinda zaiji ya gamsu kuma ta kasa sannan tabi bayan kiran Maryam d'in nan ta kasa kusan rabin awa tana zaune ta kasa kiranta domin batasan me zatace mata ba saboda Abban kar yaji abinda suke shiryawa ya hana ita kuwa tasa a ranta cewa koda ace aurenta zai mutu indai burinta na Maryam ta auri Ahmad zai cika bata da matsala zama bazawara ba damuwarta bace tunda ba'a kanta farau ba kafinta an saki wasu bayanta ma za'a sake wasu tunda tasan idan Maryam d'in ta aureshi akwai jin dad'i gani take hatta gidan da zata zauna Ähmäd ne zai gina mata..................... Sabon kiran da Maryam tai mata neya dawo da ita daga duniyar tunanin data fad'a da sauri ta mi'ke tana dirowa daga kan gadon ba arziki ta nufi kofa ta bud'e ta fice Abba daya bita da kallo ya jinjina kai kawai yaci gaba da uzirinsa ita kuwa Mama part d'inta ta shige har bedroom ta shiga toilet tai qasa da murya tana d'aga kiran tace. "Hello maryam kina jina? Ina jinki meya faru kike kirana a daren nan kinsa Alhaji zai zarge ni"? Mama na rufe baki Maryam ta fashe mata da kuka tana cewa "Mama gaskiya bazan iya ba wallahi na gaji kaina bazai d'auka ba tun daga yanxu na fara kwasar ba'kin ciki a gunsa taya kuma zan shawo kansa wallahi nikam bazan iya wannan masifar ba da kinji irin maganganun daya fad'a min d'azu Wai saiyai min dukan hallaka sabida wata shegiyar cousin d'insa ta zageni nakai qararta gurin Momy yayi min tas yace qarya nake yi nikam na gaji Mama gida zan taho bazan iya ba ha'kurina yaje karshe". Jin abinda take cewa yasa cikin kad'uwa Mama tace ''ban gane bazaki iya ba kenan ha'kura zakiyi dashi ki dawo gida ki zauna tare damu kome naji kina wata magana wacce bata gamshe niba"?. "Eh Mama gida zan taho domin zamana anan bashi da wani amfani kawai 6ata lokaci nazanyi Ahmad bazai ta'ba kallona ba balle ya soni da kinji abinda yake cewa d'azun wallahi kema abun saiyai miki ciwo a ranki baza kiso na sake koda sakan d'aya ne a gidan nan ba dan haka nikam gobe tun asubar fari zaki ganni bazan qara zuwa gidan nan ba na ha'kura da Ähmäd" ta karasa maganar tana sake rushewa da kukan ba'kin ciki. Hankali tashe Mama tai saurin girgiza kai kamar Maryam d'in tana ganinta tace "a'a kul na haneki karki kuskura kiyi wannan gangacin karna ga kafarki kin dawo gidan nan saidai idan Ahmad shima yabar gari kin gane ki qara ha'kuri yaushe ma kikaje gidan da zaki fara 'korafi ai dole saikin dad'e dama koda ma ace zai saurareki". "Wallahi mama nikam na gaji bazan iya ba haka kawai zan zauna yana yimin kallon banza shegiyar cousin d'insa tana zagina da fad'a min ba'ka'ken maganganu na cewa gidansu naje na sameta ba itace tazo ta sameni ba abun ba'kin cikin harda Khairat a ciki" takaicin maganar da Maryam ke fad'a ya gama rufe Mama ji take inama zataga Maryam a yanzu da take mata wannan sakaryar maganar da saitayi mata dukan tsiya meyasa bazata kamasu tai musu duka ba tana zaune suna zaginta idan Maryam d'in bazata iya dasu ba ita zataje har gidan taci ubansu a gaban Momyn tunda tana sane ta bari suke mata abinda suka ga dama......... Kukan da Maryam take harda shid'ewa yasa Mama ta sake harzu'kowa a masife tace "ke dan uwarki ki rufa min baki shashashar banza kawai kenan tunda kikaje uwar me kika tsaya kallo baki abinda ya kaiki ba sai yanzu zaki kirani da daren nan ki dameni da kuka dan kisa na kasa komawa barci na kwana ina tunani"?. "Nayi iya yina Mama na ko'karta kamar nayi hauka amma Ahmad ko mutum bai mayar dani ba kamar package ka cire abinda yake ciki ko wani abu mara amfani haka ya mayar dani ko saurarata bayayi gashi ya kusa tafiya inaga bazai sake kwana biyu ko uku ba gaba zai koma" dafe 'kirji Mama tai tana cewa "ya kusa tafiya kuma na shiga uku Maryam zaki d'ora min masifa da bala'i me kike son cewa ya kusa komawa bakiyi 'ko'kari kinyi wani abu dazai amfane muba"?. "Nayi wallahi nayi Mama kawai Ahmad ya fita dabam ne a cikin maza yana da wuyar sha'ani baya yin abinda bai dameshi ba baya shiga safgar daba tasa ba bayayin abinda yasan bame amfani bane a gunsa da ace Abdul-Hamid ne matsayinsa da duk haka bai faru ba wallahi ko kaffara bazanyi ba da ace shid'in ne da yanzu an wuce gurin na tareshi na fad'a masa abinda ke raina kuma nasan zai amince min amma shifa na tabbata idan yasan ina sonsa maybe karshen ala'ka ta dashi kenan kona jawo ya koroni daga gidan". "Ya koroki saboda kinje gidansu humm aiko wallahi bai isa ba zanyi magana da Auntyn nizan kirata na fad'a mata dalilin zuwanki da zamanki a gidan inyaso ita saita fad'a masa na tabbata indai yaji haka shikenan ai ko baya sonki yasan kina sonsa sannan batu ya biyo ta gurin mahaifiyar sa idan tace masa ya aureki dolensa ya amince ko baya so shiyasa nake fad'a miki ki qara ha'kuri nasara tana gaba idan gari ya waye ki saki ranki karki nuna wani abu ma ya faru ki nuna musu bariki har ita wancan yarinyar da kike magana akai ki sharesu kawai kiyi abinda ya kaiki ki manta dasu kinji"? Kai Maryam ta d'aga tana goge fuskarta tace "ok shikenan Mama na fahimta zanyu yadda kikace" "yauwa Maryam har kinsa naji dad'i ki tsaya ki nutsu kiyi abinda ya kaiki ni bari na koma kar Alhaji yaga na fito na dad'e" "ok Mama saida safe"? "Tom mu kwana lafiya" ta fad'a tana cire wayar a kunnenta tare da tsayawa tana jinjina kai ta ciji yatsa tana cewa "tabd'ijan amma lallai Maryam tsabar d'anyan kai kice zaki dawo gida batare data kin jawo hankalin Ahmad kanki ba humm wallahi bazan amince hakan ta faru ba zan kira Auntyn nida kaina na fad'a mata dalilin zuwanki gurinta sai naji me zatace zata goyi bayan abinda nace ko bayan d'anta zata bi indai ta nuna abinda yace shine take kai hum'um heyyy dan'kari akwai hayaniya a gaba da tashin hankali indai akace yaron nan ya'ki na'am da auren Maryam harna hasko ya'ki da guguwar da zata faru matukar bata umarci Ahmad ya aureki ba Maryam bari dai Allah ya kaimu goben ayi wacce za'ai'' ta karasa maganar tana fitowa daga toilet ta goge gumin datai kafin ta fita ta koma part d'in Abba ta d'auka zai sake mata magana akan kiran da Maryam d'in tai mata sai kuma taga bai tanka mata ba shiyasa tana kwanciya tai saurin komawa barci saboda karma abun ya ciyo zuciyarsa ya sake mata tambaya akan haka. •°•°•°+°•°•°• Sanin da khaleel yayi yanzu Aiman baya 'kasar kome zaiyiwa Ayrah babu me d'aukar mataki a kansa yasa gabadaya yabi ya matsa mata iskancin yau daban na gobe dabam yakai da hatta muryarsa idan Ayrah taji gabanta ya ri'ka fad'uwa kenan tun ranar daya nuna mata cewa ga abinda yake so ta amince masa ta bashi kanta zaiyi mata komai ta'ki shikenan tun daga sannan ta sake tsanarsa take jin mugun tsoron sa batasan kad'aituwarsu guri d'aya koda yana tare dasu Hajiya Khubura ne balle kuma ace gata gashi iyasu biyu ji take kamar numfashinta zaibar jikinta tsabar firgici da take tsintar kanta a ciki kullum bata samun isasshen barci saboda shi wani lokacin kamar aljani har batasan ta inda yake shigowa bedroom d'inta ba kawai saidai ta ganshi. Yauma kamar koda yaushe haka ya shigo mata d'aki cikin dare saiji tayi ana ta'ba mata jiki a firgice ta farka tana tashi zaune zatai ihu ya d'ora yatsarsa saman bakinsa yana cewa "shittt kiyi shiru ba wani abu bane ba wani abu zanyi miki ba kin gane nine fa Khaleel nazo taya ki kwana ne kawai big girl ba wani abu ba" ya fad'a yana shirin zama a gefen gadon zaro ido waje Ayrah tai zuciyarta na bugawa da 'karfi muryata na rawa ta matsa baya da sauri saboda saura kad'an ya zauna akan cinyarta kuma yana sane yai hakan a susuce hawaye yana zuba mata tace. "Dan Allah ka fita min a d'aki niba 'yar iska bace kamar yadda ka d'auke ni bana son ganinka khaleel wai me kakeyi haka ne? nayi maka kama da irin 'yan iskan matan banza da zakace kazo taya ni kwana ni bana bu'kata ka fice min a d'aki domin ban kasance 'yar iska kamar yadda ka d'auke niba" tana rufe baki ya saki dariyar nuni da cewa abinda ta fad'a nishad'i kawai ya saka shi yana kallonta yace "oh me kike nufi waye d'an iskan kenan nine"? Shiru tai a razane tana kallon yadda yake binta da wani mayen kallo ganin bata bashi amsa ba ya mi'ke daga zaunen da yake yana nufar kofar bedroom d'in ya sanya mata lock kafin ya juyo yana cewa "nan da gari ya waye babu wanda zaisan tare muka kwana da asuba zan fita na koma bedroom d'ina kinji zan baki duk abinda kike so kud'i gida mota ko yawon sha'katawa kike bu'kata da kaina zan kaiki duk 'kasar da kikace kina son zuwa komai fa da kike so babu ce kawai bazan baki ba itama da ana ganinta wallahi zan baki saboda ta ko'ina kin cika mace kalli 'kirjinki a cike sai she'ki suke cikin kyakkyawar rigar barcin ki kalli fararen cinyoyinki dubi dogon wuyanki kalli le6an bakinki masu taushi da kamshi wayyo Allah Baby kin had'u fa musamman yanzu dana tsaya ina kare miki kallo babu manyan Kaya masu rufe surarki wash Baby kin tada hankalina wallahi kalleki komai a wadace dubi hips d'inki oh my God please Baby taho guna I love you" ya fad'a yana bud'e mata hannuwan sa alamar tazo gareshi qara matsawa baya Ayrah tai tana 'kan'kame jikinta tare da sakin kukan damuwa da ba'kin ciki musamman yadda taji yana lissafa tsarin halittar jikinta ji tayi kamar ta dau'ki wu'ka ta da6a masa ya mutu kota huta ganin dayai ba daina kukan zatai ba yasa ya baro bakin kofar da yake yana tahowa gurinta dur'kusawa tai tana sake fashewa da wani mayataccen kukan tace. "Dan girman Allah khaleel karka ta'ba ni ka barni dan Allah" ko sauraron ta baiyi ba balle yace tana masa magiya bare ya ha'kura sai kanta da yazo yana saka hannu ya ri'ko nata hannnun zai mi'karta tsaye taga yana shirin ta'ba breast d'inta da qarfi da make hannunsa zata fasa 'kara ya hanata ta hanyar toshe mata baki da tafin hannunsa du'kawa yai yana d'aukarta zai nufa kan bed da ita ganin idan tai sake fa gayan nan zai cika burinsa a kanta na ganin ya lalata mata rayuwa aiko yana direta tai saurin hankad'a shi tana mi'kewa da gudu ta nufi kofar fita bin bayanta yai yana zuwa ya sake dam'karta ihu ta zunduma masa da iya 'karfin ta wanda a d'ari Khaleel ya bud'e kofa ya fita da gudu yana fita Ayrah ta karasa kofar da gudu taje ta rufe jikinta na rawa da'kyar ta iya baro gurin ta dawo tana bud'e wardrobe ta dauko Kaya kawai tasa a jikinta ta ha'kura da kayan barci hakan zaifi mata alkhairi data bari ya lalata mata rayuwa a banza koda ta koma ta kwanta bata iya barci ba sai daga baya da yake barci 6arawo ne da'kyar ya d'auke ta batare data sani ba. Khaleel kuwa tunda ya koma bedroom d'insa kasa nutsuwa yayi ko zama bai iya yiba balle shi ya samu damar komawa barcin sai zaga cikin filin bedroom d'in yake yana goye da hannu a baya babu abinda zuciyarsa take hasko masa sai surar Ayrah tsabar jaraba da yasa a ransa har wani sid'ar baki yake kamar me shan minti can kuma ya dam'ke joystick d'insa daya mike tsaye da qarfi yana runtse ido tare da cije lips yace. "Ohhh Baby zaki kisa a gidan nan indai baki amince min ba na rantse bazan barki ba sai nasha kalar d'and'anon za'kin da kike dashi daga ganinki zaki ni'ima dad'in ki wane zuma a baki dole nema ki amince min ko bakya so" ya karasa maganar yana bud'e ido ya kalli yadda har lokacin joystick d'in nasa yake mi'ke huci me zafi ya fitar yana cewa. "Bazan iya barci ba bazan iya ha'kura dake ba Baby dole na koma zanyi amfani da abinda dole ki amince min batare da kin sani ba komai zai faru nayi alkawari yau bazan rabu dake ba saina cimma burina a kanki" ya karasa maganar yana bud'e drawer ya d'auko wata kwalba ya kalla tare da jingina harda sakin murmushin mugunta kafin ya bud'e bedroom ya fita yana komawa part d'inta amma kofar a rufe ruf babu yadda zaiyi ya iya shiga d'an kwankwasa mata yai a hankali saboda dare d'aukar magana yace. "Baby please open the door" jin shiru ba'a amsa masa ba ya zagaya ya koma ta window yana zura hannunsa ya d'age labule ya ganta kwance a lullu'be ta koma barci dafe kai yayi yana sake kallonta ga 'koshi ga kwanan yunwa inama yadda tai barcin nan ace da kofar dazai shiga ko kuma d'azu ne yana zuwa shi kad'ai yasan inda zai fara ta'bawa ganin bashi da yadda zaiyi saidai kallo daga nesa yasa yaja tsaki yana barin windon ya koma bedroom haka yayita yawo yana son ya ragewa kansa zafi amma a banza har kiran sallar asuba a kunnensa tunani ne yazo masa yasan yanxu maybe ta tashi amma kuma yana tsoron kar Daddy ya fito ya ganshi bari yayi sai yaji an shiga masallaci zai lalla6a yaje kafin a fito yayi abinda zaiyi haka ya sharad'a a ransa amma yasan duk tsiya dole yaje masallaci shima idan baije ba Daddy yana dawowa zai tambayi meyasa bai ganshi ba tuna hakan yasa ya ha'kura kawai yai wanka sakamakon ya 6ata jikinsa ya tadawa kansa sha'awa a banza. Ayrah kam da abun ta farka da daren abin bai dameta ba kamar sanda gari ya waye haka tayita kuka a bedroom ita kad'ai idonta ya zama jawur fuskarta ma haka ganin d'akinta yayi haske sosai yasa ta fahimci gari ya waye yadda zataje ta d'ora musu breakfast mi'kewa tai tana shiga toilet ta wanke fuskarta ta fito tad'au hijab tai parlor babu kowa dan haka wucewa tai ta shiga kitchen ta fara aiki sauri take ma saboda batasan haka rana ta fitoba saida ta fito yanxu ta gani gashi zataje school dole ta takaita abinda zatai musu saboda karta makara a gaggauce ta kawo musu dinning ganin babu wanda ya fito yasa ta koma part d'inta ta shirya ta dau'ki hijab da handbag d'inta ta fito gabanta ne ya fad'i lokacin da suka had'a ido da Daddy daidai sun fito shida Hajiya Khubura jiki a sanyaye ta karasa tana dur'kusawa har qasa tace. "Daddy ina kwana"? Da'kyar ta iya karasawa muryarta na rawa shima kuma maimakon ya amsa mata sai tambaya daya jefo mata "ihun uban me kikewa mutane jiya da dare"? Jin tambayar dayai mata yasa a razane ta d'ago ba shiri tana kallon sa zuciyarta na harbawa da mugun 'karfi a tsawace yace "kallona nace kiyi ko amsa nake jira ki bani ubanme ya sakaki ihu da dare ki fad'a min tun kafin ki fusata ni na yanke miki hukuncin da baza kiji dad'insa ba" ya fad'a kamar zai kai mata duka yana zaro ido rai 6ace kuka Ayrah ta fashe dashi cikin tashin hankali ta d'ora hannunta aka tana cewa. "Dan girman Allah Daddy kayi hakuri idan na 6ata maka rai ka yafe min bada sona nayi ihu dan na tasheku daga barci ba". "Ok bada sonki bane to dason wa kikai ihun? Iye fad'a min dason wa kikai ihun nace ki fad'a ko saina mareki tukuna"? Ganin da Ayrah tai yana shirin kai mata marin da gaske yasa da sauri ta matsa baya tana girgiza kai zafafan hawaye suna zuba a idonta ta kasa magana ganin khaleel ya fito yasa a rud'e batasan lokacin data nuna shiba wanda a d'ari Hajiya Khubura ta zaro ido tana cewa. "Kan bala'i lallai yarinyar nan wato sharri kike shirin 'kulla masa me kike nufi naga kin d'aga wannan mitsiyacin yatsan naki kina nuna shi nufinki shine ya saka ki ihun ko mafarkinsa kikai"? Kai Ayrah ta girgizawa tace "wallahi ba sharri zanyi masa ba kuma ba mafarki nayi ba a zahiri na ganshi da dare ya shiga d'akina wai saina bashi kain......................... Cikin azama Hajiya Khubura ta gwa6e mata baki saboda karta 'karasa jin abinda take fad'a a masife tace "dan uwarki Khaled d'in ne zai shiga d'akin ki ubanme zaiyo miki wato saboda kin kawowa mutane 'kwarto gida kuma kinga asirinki yana Shirin tonuwa shine kike neman la'kawa khaleel 'karyar shine to wallahi bari kiji idan ma haushinsa kike ji nan gani nan bari babu yadda zaki dashi zama a gidan nan yanzu ya fara koda ace wannan mara kunyar Aiman d'in ne ya dawo bashi da bakin magana balle ke banza wacce ba'a mayar da ita mutum a gidan nan ba Kinga bangon nan ya fiki kujerar nan ta fiki takalimin 'kafatar me gadin gidan nan ma yafiki daraja a gurina wallahi kuma ki saurari gargad'i na a kanki duk ranar da tsautsayi yasa kika sake d'aukowa mutane 'kwarto cikin gida sannan kikece wai khaleel ne humm na rantse da Allah wallahi tallahi saina 'karya ki a gidan nan kuma na 6alla banza babu wani abu da wani ya isa yai min". Allah sarki tsabar kukan da yaci 'karfin Ayrah har wata iriyar shid'ewa take numfashinta yana d'aukewa Daddy da ransa ya gama 6aci da maganar kwarton da yaji Hajiya Khubura tana ambata yace "harda kwarto kike kawo min gida Ayrah kwarto fa? Kneeldown Ayrah tai tana cewa "wallahi Daddy ka yarda dani ban kawo kowa gidan nan ba ni kad'ai nake kwana" tana rufe baki Hajiya Khubura tace "sannu sarkin musu 'karya akai miki kenan baki kawo kwarton ba tsana tasa mukai miki haka ko"? Kasa magana ayrah tai Daddy daya rasa abinda yake masa dad'i yace. "Daga yau ta faru ta 'kare badai kin fara neman maza ba? To daki jawo min abin fad'a a gari gara nayi aurenki na huta koda me gadi ne ko kuma almajiri inyaso sai kije ki 'karata tashi kiba mutane gu kafin ki karasa kaini bango na miki duka a parlon nan" yana rufe baki Ayrah ta mi'ke jiki na 6ari ta fice daga parlon kallon Daddy Hajiya Khubura tai ganin ya shiga damuwa da yawa yasa ta saki murmushin jin dad'i a ranta tana she'ka dariya amma a fili sai tace. "Kayi hakuri Alhaji karka saka damuwa a ranka toya za'ai 'yarka ce dai tariga ta zama kangararriya bazata ta'ba dawowa daidai ba abun da yafi sau'ki kawai shine kayi auren nata ka huta amma kasan dama na fad'a maka khaleel yace yana sonta fatan baka manta ba"?. "Ba mantawa nayi ba amma taya zaki bar khaleel yaron karki me hankali da tarbiyya ya auri watsattsiyar yarinya irin Ayrah wacce ta riga tafi karfin mutane kawai ki 'kyale ya samu me hankali ya aura ita kuma zanyi magana da me gadi yanxu idan na fita ya bani sadaki zan d'aura musu aure satin sama" dafe 'kirji Hajiya Khubura tai tana girgiza kai da sauri tace "a'a Alhaji kar kayi haka babu komai shi khaleel d'in aiyasan halinta tunda ya zauna a gidan amma a hakan yace shi tayi masa yana sonta kuma zai aureta dan Allah Alhaji kar kayi wannan gangacin karka kar'bi kud'in me gadin nan indai sadaki kake so Khaleel zai tura maka yanzu" kaiya girgiza yana cewa "a'a tunda kince haka ki bari kawai mubu abun a sannu shikenan Allah ya shiryar da ita shi kuma dazai dau'ki 'karangiya Allah ya bashi hakuri da juriyar iya zama da ita". Wani murmushi Hajiya Khubura ta saki tana kallonsa tace ''amin Alhaji Amin Allah ya amsa muje kayi breakfast lokaci yana 'kure maka a tafiya office" kaiya girgiza yana cewa "no barshi kawai idan naje can zanyi". "Ok to muje na taka maka" ta fad'a tana sake gyara ri'kon kayan aikin dazai tafi dasu office takardu da wasu abubuwan suka fita saida taimai rakiya har jikin motarsa ya tada motar yabar gidan duk tana kallo sannan ta juyo da murnar kwanan nan zata zama millionaire a dinning samu khaleel da Abidah suna karyawa zama tai tare da sauke numfashi tana kallon sa cikin fad'a tace. "Khaleel kai d'in ubanme yakai ka d'akin wannan yarinyar me kaje nema har take neman d'ora maka sharri kuma tsabar shashanci kana jinta kayi shiru da ace bana gurin yadda wannan yarinyar take da baki wallahi baka isa ka ceci kanka ba so'ko'kon banza sakalin wofi a ido kamar zakai zarra amma ina zuciyar a mace take". Had'e rai khaleel yai yana kallon Abidah datai shiru tana sauraron zancen da sukeyi a fusace yakai mata duka yana cewa "ke dan ubanki zaman me kike zaki bar gun nan kosaina 6allaki" ya fad'a yana sake kai Mata sabon duka da gudu Abidah ta mi'ke yayin da Hajiya Khubura ta buga masa wata uwar harara tana cewa "sakalin asara yanzu ka kasa yiwa wancan figaggiyar amma da yake Abidah 'karamar dangarka ce me dad'in tsallaka shine harda dukanta dan kawai ta tsaya tana sauraron magana". "To tsakani da Allah Umma dan uwarta ni sa'an tane a ri'ka min fad'a a gabanta kuma tayi fiki-fiki da kunne tana saurara salon ta raina ni"?. "Ba wani ta Raina ka saidai ka raina kanka niduk ba wannan ne damuwa taba tambayar da nake meyasa ka shiga d'akin Ayrah ina ruwanka da ita so kake ka jawo min bala'i idan tai ciki ko bakai bane tunda kaita sani cewa zatai kaine kayi mata to wallahi ka shiga hankalinka ba ruwana kana jidai ko? Ka kiyayi kanka da sharrinta ka daina koda kallonta idan kuma matsuwa kayi ka aureta fad'a min naji"? Kaiya girgiza yana ta'be baki yace "ko d'aya niba aure kwana kusa a raina kawai dai yarinyar tana burge nine shiyasa na damu da ita amma ba soba". "Aiko indai har a ranka kanaji ka damu da ita khaleel dole saidai a d'aura muku aure". "Nifa Umma ba yanxu xan aureta ba shikenan abar maganar insha Allahu bazan sake kulata ba har sai naga lokacin dana sakawa kaina nayin auren yazo sannan zanyi miki magana" numfashi Hajiya Khubura ta sauke cikin jin d'an dama-dama tace "ok shikenan hakan yayi amma ka tabbata abinda ka fad'a min gaskiya ne karna sake ji ta kawo 'korafin ka". "Eh na amince Umma zan kiyaye" ya fad'a yana kallonta harararsa tai zatai magana yai murmushi yana cewa "da gaske fa nake babu abinda zai sake shiga tsakanin mu dama niban ta'ba zuwa inda take ba jiyan ma kasa barci nayi kuma dana shiga bedroom d'in nata ba wani abu nayi mata ba na fito please Umma ki fahimce ni man kamar ba mahaifiyata ba kin tsaya sai tuhuma ta kikeyi alhali kinsan abinda zan aikata da wanda bazan iya aikatawa ba haba dan Allah kar kisa na fara tunanin wani abu dabam man"? Jin abinda yace da kuma sauyawa na rashin jin dad'in dayai ta gani akan fuskarsa tace "ok ok na fahimta sosai khaleel na gane shikenan ya wuce Allah ya kaimu lokacin daka d'iba na bikin naku Allah yasa ba dogon lokaci bane nidai na matsu naga dukiyar nan ta zama mallaki na ta dawo hannuna" mi'kewa yai yana cewa "saurin me kike? Zata dawo ai harsai kin gaji da ri'keta a hannnun naki kin kai ajiya banki" yana fad'in haka ya fita a parlon shiru Hajiya Khubura tai tana tunani wato khaleel ne ya shiga d'akin Ayrah da dare idan ta fahimta har ya nuna yana son wani abu a gurin ta itakuma tai masa ihu Daddy yaji yanzu yake tambayar ta itama tasan bazata ta'ba kawo kwarto gidan ba kawai ta fad'a ne saboda tasa Daddy ya fusata ya wulakanta Ayran kuma yayi shikenan burinta ya cika..........✍️Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë 🌺. Be with me at always my lover's nagode da kulawarku gareni godiya sosai sosai godiya. TYPING 📲 Wed apr/2025 09:44am YUSRAH MUSA ABUBAKAR ✨✨. 👑 ROYALTY 👑 ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫 Home of hospitality and harmony gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan ta. S✓W✓E ©©Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë mai tambarin yma dutse Jigawa state new world sabuwar duniya kuzo kuyi kallo dad'i yana Jigawa garin ilmi garin addini zaman lafiya Jigawa. Dedicated to my daughter FATIMA ZARAH SHAMSUDDEEN ABDUR-RAHEEM DUTSE. *** * *** 13~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Khaidinah. Bismilllahir Rahmanur Rahim 📿. @YUSRAHMS CE Page 25 & 26 Kamar yadda Mama ta fad'awa Maryam cewa zata kira Momy suyi magana washe gari ta kirata tunda Momy taga kiran Maman ta fahimci Maryam ta kirata ta fad'a mata abinda ya faru jiya da farko kamar bazata d'aga ba saboda bata son hayaniya sai kuma tayi tunani indai bata daga ba Mama zata gasgata abinda Maryam ta fad'a mata koda ace 'karya ta shirya gara ta d'aga taji meya faru lokacin har Mama ta gaji da kira kusan missed call goma ta ha'kura Momy tai kiranta dama a lokacin ta gama d'aukar fushi shawara take yankewa a ranta kawai ta d'auko mota taxo gurin Momyn suyi magana ido da ido sai tafi fahimtar ta akan a waya tana cikin wannan halin taga kiran Momy jikinta har rawa yake ta d'aga ko sallama babu tahau fad'a "yanzu aunty dan Allah haka ake rayuwa wanne irin abune wannan taya Maryam dan kawai tazo muku ziyara su Khairat zasu sakata a gaba da zagi dacin mutunci shi kuma Ähmäd da hankalinsa yad'au karan tsana ya d'ora mata haba dan Allah kina kallo haka yake faruwa itafa Maryam ba haka kawai tazo gidan nan ba tazo ne akan kisa Ahmad ya aureta wannan shine dalilin ba wani abu ba maimakon hakan sai wulakanci ne yake biyo baya daga an shirya abun alkhairi". Mamaki ne ya kama Momy sosai oh wato Maryam zuwa tai nan d'in dan Ahmad ya ganta ya aureta bayan shi yana da wacce yake so kuma koba haka bama tasan Ahmad bazai aureta ba koda ace bashi da wacce yake son balle yana da za'bin ransa ta dad'e da fahimtar Maryam tana da halin da Ahmad baya so ita kuma tace abinda mutum ya nuna mata baya so shi zatai masa shiyasa tun farko basa shiri da Ahmad ko kad'an danya tsani raini baya zana inuwa d'aya da fitsararre mara jin magana................ Dawo da ita daga duniyar tunanin data fad'a Mama tai tana cewa "Hello Aunty Hauwa kina jina"? Kai Momy ta jinjina tana cewa "Eh ina jinki meya faru kuma bayan hakan naji wannan me dame ta fad'a miki"? Haushi ne ya sake rufe Mama a hasale tace "kuma kina jina Aunty amma kikai shiru bayan na fad'a miki dalilin zuwan Maryam d'in zaki ce meya faru wato saboda laifin Ahmad ne shiyasa bakya so na fad'a"?. "Ok rashin kunya zaki min kenan'? Momy ta fad'a ranta a 'bace. "Niba rashin kunya zanyi miki ba tambayar taki ce ta 6ata min rai sabida na fad'a miki ga dalili amma naji ko saurara ta bakya yi". "Wanne dalilin ne"?. "Nace miki Maryam tana son Ahmad ne dalilin zuwan ta gidan shine tana so ya ganta ya kamu da sonta ya aureta a qara karfin zumunci wannan shine abinda ya kawota gidan ba komai ba". "Ita Maryam dince take son Ahmad"? Momy ta tambaya tana jiran taji amsa cikin 'kwarin gwiwa Mama tace "kwarai kuwa shine abinda yasa ta dawo nan domin suyi magana dashi idan ya amince ya aureta domin ta dad'e tana sonshi tana so yace yana sonta tunda shi ya'ki fad'a shiyasa ita tazo ta fad'a masa ta dad'e tana sonsa ba abun kunya bane dan mace tace tana son namiji yin hakan kwalliya ce" jin abinda Mama tace yasa Momy tai shiru tasan abun da kamar wuya amma saboda kar tace itace bata so ko taiwa abun fahimtar daba haka bane sai tace. "Ok shikenan Halima karki damu indai haka ne zan samu Ahmad d'in nayi masa magana duk yadda yace zakiji na kiraki" jin abinda Momy tace yasa Mama sauke numfashi cikin jin dad'i tace "yauwa Aunty yanzu naji magana shikenan nagode saina jiki ina jiranki dan Allah karki manta"?. "Ok bazan manta ba sai anjima" Momy ta fad'a tana cire wayar ta ajeta a gefenta kenan taji taku da sauri ta waiga ganin Ahmad a tsaye ya mugun had'e rai yasa ta d'an rufe ido ta bud'e tasan yaji komai tunda batasan lokacin tsayuwarsa a gurin ba shima a nasa 6angaren hakan take duk maganar da Mama take yaji kowacce kalma d'aya bayan d'aya kallonsa sosai Momy tai taga yakai ma'kura wajen 6acin rai murya a tausashe irin na ambato tsakanin d'a da uwa tace "Ahmad yaka tsaya anan shigo mana zonan dama magana nake so muyi dakai yanzu kuma sai gaka ka shigo karaso gurina" huci ya fitar yana cire hannunsa daga cikin aljihun wandonsa ya kalli kofar part din su Khairat yasan Maryam tana ciki ji yake kamar ya shiga yai mata d'an banzan dukan da a azaba zatasa tace ta tsane shi daga soyayyar da take masa tsabar rainin hankali shine zai sota ya zauna da ita aiko baida wacce yake so bazai amincewa Maryam ya yarda ta zama uwar 'ya'yansa ba balle yana da wacce yake jinta kamar ransa yake mafarkinta a koda yaushe wacce ya d'auketa rayuwar sace ya tabbata without her, his life will difficulty zai shiga tashin hankali wanda baya fatan zuwansa.......................... "Ahmad zonan" yaji muryar Momy ta katse masa tunani dawo da hankalinsa kanta yai yana kallonta kamar yadda itama ta 'kureshi da kallo 'karasowa yai yana zama kusa da ita muryarsa ba normal yadda ta sanshi ba yace. "Barka da safiya Momy fatan kin tashi lafiya"?. K'ara kallonsa tai karo na uku tana d'an girgiza kai tare da sakin murmushi tace "lafiya kalau na tashi Ahmad dama yanzu muke magana da Halima bansani ba ko tun daga farkon maganar tamu ka tara ko kuma karshe ne banace ba fatan kaji maganar da mukai da ita akan zuwan Maryam dukda nasan kai kana da wacce kake so batun yanzu ba amma sakamakon kar nace mata a'a taga kamar nice bana son abun shiyasa nace ta bari sai nayi maka magana tunda Allah yasa kaji komai yanzu me kace za'bi ya rage naka nasan daga baby baka marmarin qara wata saidai kai mijin mace hud'u ne idan kaga kanada bu'katar 'kari sai kayi magana nasan me zance mata koba yanxu ba zuwa gaba saika aureta hakan yayi maka"? Kaiya girgiza batare daya d'ago ba yace. "Momy kece kika haifeni kinfi kowa sanin halina kinsan abinda zan aika da wanda bazan iya aikatawa ba koda ace bani da wacce nake so bazan iya auren Maryam na zauna da ita ba badan tai min wani abu ko tana da wani mugun hali ba a'a kawai nidai batai min ba matsayin mata wannan shine idan Mama ta sake kiraki ki fad'a mata sa'ko daga ni nace a'a indai danni Maryam tazo gidan nan to takoma gidansu karta 6ata lokacinta domin bazan ta'ba sauraron taba karta yaudari kanta niba wanda za'aiwa wargi bane banyi kama da masu yin wasa ba idan na fad'i magana gaskiya ne abinda yake fitowa tun daga 'kasan zuciyata na fad'a Maryam cousin d'ina ce bai kamata ace wani sa6ani ya shigo tsakanin mu wanda baza'a ji babu dad'i ba sannan ni bazanyi abinda zai takura niba ki fad'a mata haka" tunda ya fara magana Momy ke jinjina kai dama tasan amsar kenan kuma ta tabbata yanxu idan ta kira Mama ta fad'a mata bazata yarda ba gani zatai wannan maganar ba Ahmad neya fad'a ba itace ta zauna ta shirya zata so ace Ahmad d'in zaije da kansa har gida yaiwa Maman bayani da kansa yadda zatasan matakin da suke saidai idan ma zata jarraba kiran nata ta fad'a mata yadda sukai dashi koda bazata yarda ba numfashi ta fitar tana kallon sa tace. "Na fahimta Ahmad dama nasan haka zai faru to amma saboda kar nacewa Halima kana da wacce kake so taga kamar nice bana son had'in da take bu'kata na aure tsakaninka da Maryam shiyasa na fad'a maka kaga na fita daga zarginta yanxu ina da babbar hujjar da zanyi mata bayani idan bata fahimce niba zakaje har gida kai da ita ka fad'a mata komai"?. "Zanyi hakan Momy ina Khairat suke"?. "Suna part d'in Maminsu yanxu basa kwana anan". "Ok" kawai yace yana mi'kewa ya fita shiru Momy tai farko har tayi tunanin kiran Mama ta fad'a mata a take sai kuma tunani yazo mata idan ta kirata yanzun nan ta fad'a mata tofa zatace bata wani fad'awa Ahmad ba itace bata so shiyasa ta yanke hukunci da kanta tunanin hakan yasa ta mayar wayar ta ajiye ta fasa kiran nata gabadaya bari Ahmad ya sake shigowa ta fad'a masa yaje gidan Maman da kansa ya fad'a mata abinda ke ransa zaifi zaman lafiya kuma itama Momyn zata fita. A wunin ranar su Khairat basu le'ko part d'in Momy ko sau d'aya ba koda suka dawo daga school part d'in Mami suka sake zarcewa acan sukai komai sai dare shima Mamin ce tace musu su koma part d'in Momy su kwana basu nuna mata dalilin dawowrsu nan d'in ba kawai da tace su koma can ba musu suka tashi suka tafi a bedroom suka samu Maryam tana waya sai dariya take tana doka qafa babu wanda yai magana a cikinsu da sukai mata sallama bata amsa ba sai wani irin ba'kin kallon qasan ido data aikowa Baby kamar ta tashi ta rufeta da duka ganin basu sake bi takanta ba sun kwanta yasa ta sau'ke waya tana kallon dukkan su biyun tace. "Meye hakan wannan da'ki'kancin fa malamai ku tashi min anan" Maryam ta fad'a a masife dama a turare take dasu yaye bargo Khairat tai tana cewa "me akai miki daga shigowar mu kika fara neman mutane da fitina"?. "Au abinda zakice kenan saboda wulakanci"?. "Toya kike so nace idan bance miki haka ba"?. Tsaki Maryam taja tana cewa "idan ba hauka ba taya zamu kwana mu uku akan gado d'aya kamar a garin mahaukata nifa a gidan mu ko mu biyu bama kwana ni kad'ai ce a bedroom d'ina ban saba da rayuwar 'kunci ba fatan kun gane"? jin abinda tace yasa Khairat tashi zaune tana cewa "me kike nufi"? Da qafa Maryam ta ta'bo Baby tana cewa "ga wacce nake so ta tashi tabar nan ta koma nasu part d'in ta kwana domin bata isa na kwanta tare da ita a gado d'aya ba" kai Khairat ta girgiza daidai Baby ta tashi zaune ta sauka akan gadon tana aje bargon ta kalli Maryam data had'e fuska tace. "Dama nasan karshen zancen dan ni kikace haka sabida ni kike wannan maganar kwantar da hankalinki ni ba'a tashin hankali dani ga bedroom da gado nan ki kwanta kiyi barcinki Allah ya tashe mu lafiya" Baby ta fad'a tana shirin fita Khairat tace "Baby karki fita dawo mu kwana" kai Baby ta girgiza tana cewa "a'a Aunty Khairat karki damu kiyi kwanciyarki saida safe matsalarta nice kuma na fita Allah ya kaimu safiya muna tare ai" ganin da gaske fita zatai yasa Khairat mi'kewa tana kallon Maryam tace "yanxu tsakaninki da Allah ke a ganinki kin kyauta duk shariya da karar da Baby take nuna miki saikin kaita bango tun tana ganin girmanki kisa ta daina gani"? Ta'be baki Maryam tai tana kwanciya tace. "Ta daina ganin girman nawa man waya damu itace take wahala bani ba kafinta ana ganin girmana sannan bayanta za'a samu masu ganin girmana Kinga ko aitayi ta banza idan tace zata kawo min raini kuma nayi mata shegen duka ba ruwana da gidansu nazo wallahi 6al6alla mata ga6o6i zanyi kuma na 6alla banza". "A ganinki kenan amma ba haka bane idan tsautsayi yasa kika ta'ba Baby wallahi kinji rantsuwa ko saidai kibar gidan nan jikinki a kumbure domin ya Ahmad bazai 'kyale kiba" ta'be baki Maryam tai tana jan tsaki tace "waye kuma Ähmäd a ina yake aiko wallahi kodan abinda kika fad'a saina daketa saboda Naga irin mataki da kike fad'ar zai d'auka". "Ok tunda har marmari kike ki gwada dukan nata zakiga abinda zai biyo baya Nina barki lafiya saida safe" Khairat ta fad'a tana ficewa da harara Maryam ta rakata tana cewa "ku jira shigowa gidan nan matsayin matar Ahmad d'in saina gasa muku gyad'a a hannu saikun raina kanku a hannuna takurar da yake muku yanzu nafila ce idan na shigo ruwa ma bazaku iya shaba a gidan nan kuma zaku gani" tana rufe baki Khairat ta le'ko tana cewa "bakinki ya fad'i a 'kasa aiba tafiya nayi ba dama na tsaya naji me zakice shine kike jawo mana mugun alkaba'i ko saidai ya koma kanki indai dan ki haddasa fitina kike burin shigo mana gida insha Allahu bazaki auri ya Ahmad ba har abada" tana fad'in haka ta ja kofar da karfi gamm ta rufeta har saida Maryam ta toshe kunne tana cewa "humm Khairat kenan naki wasa ne yarinya ki zuba ido a yayin dazan shigo saiki hana wallahi kodan ku biyun nan saina auri Ahmad naci uwarku son raina muje zuwa koni koku" komawa tai ta kwanta tana sake gyara kwanciyarta taci gaba da maganganu daga wannan tace wancan ita kad'ai ba kowa balle wadanda take yi dansu tace suna jinta. Baby tana bedroom a kwance taji an turo kofa da farko tayi tunanin Mami ce saida taga Khairat ta shigo fuska babu walwala ta karaso tana zama ta kalli Baby wacce itama take kallonta da mamaki tace "Aunty Khairat ya haka meyasa kema kika fito da kin tsaya kun kwana tare"? Kai Khairat ta girgiza tana cewa "haba Baby akan me zakice min haka dawa nake kwana da badake bane to kuma dan wata tazo sai yazama dole mu raba gurin kwanciya ai indai kikaga mun daina kwana tare to ki tabbata daya daga cikin mune yai aure koni koke" numfashi Baby ta sau'ke tana cewa. "Amma aida nine bata son kwanan ba dake ba shiyasa na taho na bata guri domin bana son yawan hayaniya". "Akan me zan tsaya mu kwana tareda da ita nake kwana ba dake bane zuwanta kuma sai yasa na daina kwana dake"?. "Eh za'a iyayin hakan kafin ta tafi ba'ko ra6a ne duk irin dad'ewar da zaiyi wata rana dole saiya tafi shiyasa bana so ace dan tazo zama nadan lokaci abinda bakai ya kawo ba na laifi dana ganin dama abi a tashi hankula har manya su shiga ciki dan haka kawai ki 'kyale Aunty Khairat dan Allah ki daina biye mata kuna yi na tabbata idan tai miki kikai mata shiru shikenan gobe bazata qara ba" kai Khairat ta d'aga tana kallon baby da murmushi tace "kinsan me baby? Wallahi shiyasa kike burgeni saboda sau'kin kanki babu ruwanki kayanki ma bai rufe miki ido ba balle kisa rai akan na wani na gane nima naki salon zan d'auka zanyi amfani da abinda kikace min bazan sake biye mata ba indai ba maganar arziki ko maganar zumunci zamuyi ba". "yauwa Aunty Khairat haka nake so naji wallahi har kinsa naji dad'i a raina kinga yanxu kowa ya huta bazata taga mun takura mata ba muma bamu shiga safgarta ba". "Eh hakan zamuyi harta gama operation d'inta ta koma babu me sake shiga safgarta indai ba maganar arziki za'ai ba". "Operation d'in me tazo yi anan gidan kuma"? Baby ta tambaya da mamaki "hum operation take man idan ba haka ba meta zoyi ko d'agawa mutane hankali ni banga abun damuwa anan ba amma tunda haka ta za'ba shikenan dai" Khairat ta fad'a tana hawa gadon kusa da Baby ta kwanta tana jan bargo babu wanda ya sake magana har barci ya d'auke su. Washe gari dan kar Mami taga cewa ba'a part d'in Momy suka kwana ba tayi musu fad'a tun asuba suna idar da sallah suka fita zuwa part d'in Momy sukai zamansu sukai azkar har gari yayi haske tar sannan suka tashi suka koma part d'in Mami suka gaida ita sun dad'e kafin suka dawo sashin Momy da suka shigo bata nan dinning suka wuce kowa tai serving abinda take so ko fara ci basuyi ba Maryam ta karaso gurin ti'kas-ti'kas tana shan 'kamshi tazo ta zauna tare da d'ora 'kafa d'aya kan d'aya tana kallon Baby tace. "Ke yi serving d'ina". Kamar bada ita take ba haka Baby ta manna mata ko d'agowa batai ba balle tasa ran zatai abinda tace din kai Maryam ta jinjina tana mayar da kallonta kan Khairat tace "ki sakata tai serving d'ina tunda ni ta raina ni ban isa da ita ba" mamaki ne ya kama Khairat har batasan lokacin da tace "lallai Maryam da wargi kike sannunki da kokari Babyn ce zatai serving d'inki ko kuma bayi masu hakkin kula da hakan kike magana"? Kafad'a Maryam ta d'aga tana cewa "wadanne irin bayi kuma bayan ga babbar baiwa a gabana da ita Babyn nake ko tafi 'karfin nasata aikin ne"? Jin abinda Maryam ta fad'a yasa Khairat tai dariya tana cewa "taya zan baki amsa amma ido ba mudu ba yasan kima ki kalli Babyn sosai idan tayi miki kama da wacce aikin serving ya dace da ita sai tayi miki" kallon tsaf Maryam taiwa Baby tana cewa "ta dace d'ari bisa d'ari domin batai min kama da kowa ba sai wula'kantacciya 'kas'kantacciya yanxu kin gane"? Ta tambaya tana qure Babyn da kallo taga yanayinta amma ga mamakinta sai taga ko karasa kallonta Baby batai ba kamar bata mayar da ita mutum ba ji tayi takaicin shariyar datai ya kamata a fusace ta janye plate d'in dake gaban Babyn tana cewa. "Sai kiyi serving d'in wani kici amma wannan dai ya zama haramiyarki" ta fad'a tana d'aukar wani spoon d'in ta fara ci tsananin mamaki ne ya kama baby wato tsabar neman masifa bata kulatan ba amma bazata barta ba saitai abinda zata tanka mata humm yau kuwa zata gwada mata man nin hauka bazata koda nuna ta damu ba sharewa babay tai tana tashi ta dau'ki wani plate d'in tai sabon serving tana gamawa ko komawa ta zauna batai ba Maryam tai wuf ta janye plate d'in ta turo mata ainishin nata na farko tana cewa "ga jagwalgwalon kinan saiki cinye dama nayi hakan ne dan kiyi serving d'in nawa ko bakya so" murmushi Baby tai kawai tana qara d'auke kai daga saitinta wanda Khairat da tafi babyn jin d'acin abinda Maryam d'in tai mata tace. "Wai dan Allah Maryam me kikeyi haka ne meyasa bakya neman zaman lafiya duk kawar dakai da baby take miki saikin shiga safgarta gaskiya bakya kyautawa wannan abunfa da kike ya Ahmad yana sane bashi kike ci akwai ranar da zaki kwashi adahin ki a gurinsa" baki Maryam ta ta'be tana hura hanci a gadarance tace "a gurin wa zan kwashi adahin? Humm indai a gurin Ahmad ne saidai na kwashi nishad'i kin gane dama ni ina son bashi I love credit wallahi ba abinda ya isa yai min domin ni baku bace bazai takani na 'kyale shiba". Kai Khairat ta jinjina tana cewa "Ok haka kikace ko shikenan zakiga you love credit Allah ya taimaka kici gaba dayi wata rana zaki dana sani dama duk yadda akai da jaki sai yaci kara lokacin dazai taka kin ya gurjeki muna kallo" wata uwar harara Maryam ta sakar mata tana jan tsaki tace "ya taka wa? Ai na rantse da Allah Ahmad bai isa na tsaya ya dakeni ba ko 'kasa ce abinci na ni nafi karfin wulakancin sa". "Shiba wulakanta ki yake ba kawai yana nuna miki hanyar shiriya ne wacce zakibi amma tunda kince haka ba damuwa nidai ina qara tuna miki kibi a sannu wata rana zaki dana sani". "Wallahi ba ranar da zata fito ta fad'i wacce zanyi nadama a cikinta abinda nake aikatawa shine daidai saina hanaku jin dad'i harsai kun sallama min" ta fad'a tana sake aikawa da Baby harara wacce batasan tanayi ba ita kam hankalinta na wani gurin dabam daidai Ahmad ya shigo ya nufi inda Momy take xaune acan parlor wani irin kallo Maryam ta bishi dashi a ranta tana fad'in "wayyo Allah na dan Allah kalleka Ahmad kalli 'kirar jikinka me d'aukar hankali tana son she'ke ni inaso naga jikinka a bayyane zanso naganka batare da rigaba tabbas ina 'kwadayi idanuwana suyi tozali da kyakkyawan jikin nan naka indai baka amincewa soyayya ta ka aureni ba huuuuh ta fitar da huci tana sake d'agowa ta zuba masa ido yadda yake magana ma kad'ai abin kallo ne komai nasa cikin aji da tsari yake yinsa" numfashi ta fitar tana cije lips ta jinjina kai tana sakin murmushi lokaci guda ta shiga wani yanayi duk abinda take Khairat na kallonta kamar zatai dariya sai kuma ta maze itama tana kallo inda Ahmad d'in yake zaune a ranta tace "humm lallai wato Maryam son Ahmad take ko mene nayin wannan abubuwan aiko indai tsautsayi yasa ta kamu da ciwon sonsa ta had'a kanta da wahala ta d'auko damin daba saukewa jin 'kak'karfar ajiyar zuciyar da Maryam ta sauke yasa Khairat dariyar da take 6oyewa ta fito fili rufe baki tai ganin irin kallon da Maryam d'in take aiko mata dashi tace. "Tofa Maryam anya da gaske ne"? A kaikaice Maryam tace "da gaske ne me"? Murmushi Khairat tai tana cewa "da gaske ne kina son Ahmad"? Jin tambayar datai mata yasa ta had'e rai tana cewa "meyasa kika tambaya bayan kin sani"? Gira Khairat ta d'age tana kallon ta tace "mena sani ni bansan komai ba shiyasa na tambaya saiki fad'a min idan 'kaunarsa kike". "Eh 'kaunarsa nake sonsa nake yanzu kin sani"?. "Uhm na sani yanzu amma aurensa zaki kome"?. "Toda me kike tunani zanyi soyayya kad'ai dashi ne aurensa man zanyi zuba ido ki gani" zaro ido waje Khairat tai tana rufe baki da sauri ta danne dariyar data taso mata da'kyar tana d'an tari tace "masha Allah ashe kwanan nan zamu sha biki kenan ko"?. "Yes fad'i ki 'kara babu fashi aure kamar na aureshi ne kuma zaki zama sheda ranar dana aureshi zan tuna miki da wannan maganar". Kai Khairat ta kad'a tana cewa "ok Allah ya kaimu lokacin mukam yan shan biki ne da zuwa wajen dinner su gwangwaje". Cikin nishad'in maganar da suke Maryam ta rausaya kai tana cewa "tabbas zaku sha idan ma isgilanci kike min insha Allahu Ahmad shine mijina shi zan aura saiya ranki"?. Dariya Khairat tai tana cewa "ni raina babu komai fes yake sai alkhairi kinsan bazan yi miki ba'kin ciki dan kince ke ya Ähmäd zai aura ba ko?. "To Khairat idan zaki min ba'kin cikin ma kezaki d'orawa kanki wahala a banza nikam na riga na tsallake rijiya da baya domin ya riga yasan da maganar ma kuma bai nuna bai amince ba saiki fara shiri tun yanzu saboda kar lokaci ya 'kure miki tunda neman d'orawa kanki wahala kike yi". Ta'be baki Khairat tai tana girgiza kai tace "meye abun d'orawa kai wahala kawai dan kin aureshi idanma baki aureshi ba ina zai auri wata nidai kinsan 'kanwarsa ce ba aure ne a tsakanin muba balle kice zanyi kishi dake saboda kince kina sonsa idan haka kike nufi"?. "Oh aina d'auka kina 'kanwar tasa ma zaki kishin dani ne kodan idan ke baki ba wannan ballagazar zatai tunda ita akwai auren tsakanin su cousin d'insa ce" ta fad'a tana aikawa da Baby muguwar harara cike da tsananin kishinta da taji ya kamata lokaci guda had'e da tsanar Babyn kai Khairat ta girgiza tana cewa "A'a ita kam babu aure a tsakanin su domin baby ba ya Ahmad zata aura ba kuma shima ba ita zai aura ba karma ki sake wannan maganar ba ruwan Baby da Ahmad kawai ala'ka ce ta jini amma ba soyayya ba" jin abinda Khairat tace yasa Maryam sauke sansanyan numfashi cikin jin dad'i har tana kallon Babyn da murmushi akan fuskarta muryarta normal kamar yadda zatai magana da Mamanta tace "humm Allah ya taimake ki baby kike sunan naki ko beblo kin hutar da kanki gara kar zuciyarki ta kamu da sonsa ki d'auke hankalinki karma ki fara tunanin hakan idan auren kike so ga Abdul-Hamid nan kunfi dacewa dashi sosai fiye da Ahmad kije ki kalli kanki a mirror Abdul-Hamid shine tsaranki shine zai iya d'aukar nonsense d'inki ba Ahmad ba domin shi d'an gayu ne me aji da 'kasaita nice na dace dashi da tsarin rayuwarsa nice zan tarairaye shi na soshi na nuna masa 'kauna kamar zan mayar dashi ciki amma bake me siffar gidadawa ba" Maryam na rufe baki Baby ta mi'ke tana barin dinning d'in batare data koda kalli inda Maryam d'in take ba balle ta nuna abinda take fad'a ya dameta ko tsayawa batai ta ta fice daga part d'in gabadaya ta tafi part d'in Mami. Tana fita cikin matsuwa Maryam ta kalli Khairat tana cewa "ke Khairat ina jinki bani labari da gaske ne Ahmad baida budurwa baida wacce yake so ko kin fad'a ne dan kiga yadda zanyi"?. "A'a bana fad'a ne dan dad'in baki ba da gaske nake miki ya Ahmad baida budurwa ko kusa bai fara soyayya ba maybe Sai gaba" farin ciki ne ya rufe Maryam ta sake 'kar da murya tana cewa "to amma baku ta'ba ganin ya nuna alamar yana da itan ba"?. D'an tsaki Khairat taja saboda maganganun sun fara isarta tace "ke nifa ban sani ba inace gashi can a gurin Momy suna magana mezai hana kije ki tambaye shi kyazo ki takura min ni nasan yana da budurwa ko baida ita ne". "Humm Khairat kenan kinada abun mamaki kamar kin manta waye Ahmad ke ganinki yanxu kina da tabbacin idan na tambaye shi zai bani amsa jin kansa yayi yawa kamar na wancan yarinyar"?. Tabe baki Khairat tai tana kallo wajen inda yake tace "A'a ban sani ba ki gwada sa'arki maybe ya tsaya ya saurareki abun dace ne auren mace da ciki kinsan zan iya cewa bazai saurare kiba kije ya saurareki kizo kina yimin kallon ma'karyaciya amma gashi can kije ki gwada" tana fad'in haka ta mi'ke itama tana fita daga part d'in shiru Maryam tai tana kallon Ahmad da hankalinsa yake kan abinda Momy take fad'a masa a ranta tace "haba Ahmad! Haba my husband🤔 taya kake tunanin zan barka kalli kyau iya kyau ta ko'ina ka cika namiji kwarjini jarumtaka humm wash Allah ubangiji kana gani na ka cika min burina akan Ahmad ya Allah ka sanya akwai hukuncin aure tsakanin mu Allah yasa bani da wani mijin bayan kai dakai nake so nayi rayuwa kaine komai nawa ina sonka" ta fad'a tana bud'e idonta dake rufe kamar ance Ahmad ya d'ago aiko karaf suka had'a ido dashi murmushi ta sakar masa tana d'aga masa hannu alamar barka kaiya d'auke daga saitin ta yana mi'kewa yaiwa Momy sallama ya fita da kallo Maryam ta bishi harya fita kamar zatai ihu tsabar ba'kin cikin wannan halin ko'in kular da yake nuna mata ji tayi hawaye yana taruwa a idonta da sauri ta kifa kanta a table d'in dinning d'in saboda kar Momy ta gani itama Momyn bata kula da ita ba hankalinta bai kawo kan dinning d'inba shiyasa bata ganta ba gashi lokacin breakfast d'inta bai karaso ba balle idan tayo wajen gurin ta ganta haka ta 'karaci zubar da hawayenta ta ha'kura tana mi'kewa ta shiga bedroom. ••°°••°°••Yau tunda Ayrah tai sallar asuba bata sake komawa barci ba tana garden tana wankewa Abidah da Hajiya Khubura kayansu a ranar wuni tai tana wankin ko karyawa batai ba har karfe hud'u da rabi da yake ranar period takeyi ba sallah zatai ba shiyasa ma tunda ta fito garden d'in bata sake komawa ciki ba saida ta gama ta tattara komai ta d'ebe wadanda suka bushe ta shiga dasu ganin babu nefa sun d'auke kawai ta aje da nufin koda dare suka kawo saita goge musu duk zirga-zirgar da Ayrah take Abidah tana kallonta har saida ta gama komai ta fito daga part d'in su Abidan tana kokarin shiga nata tai wanka Abidah ta daka mata tsawa tana cewa. "Ke dabba kinfi karfin kizo kice min kin gama kenan saboda da gaki isasshiya ko"? Juyowa Ayrah tai ranta a 'bace tace "a tunani na keba makauniya bace ai kina ganin abinda nake yi ba'aiwa me ido gafara idan baki gode min abinda nai miki ba bazaki tsine min ba" gwalo ido Abidah tai tana cewa "uban waye zai gode mikin amma badai niba Allah ya sauwake nace miki koda sannu ne balle godiya ked'in banza wai ma tsaya nayi miki tambaya da yaushe raini ya shiga tsakanin mu har haka Ina magana kina kallona kina mayar min da martani"?. "Tambaye nidai na fad'a miki abinda yasa nake kallonki ina fad'a miki magana isa nayi". "Au isa kikai? Humm kan masifa da bala'i ni kike fad'awa haka tabd'ijan aiko wallahi yau sai naci uwar uwarki saikin gane ruwa ba sa'an kwando bane" ta'be baki Ayrah tai tana wucewa batare data sake bi takan taba tsalle Abidah tai tana cewa "ke dan uwarki dan ubanki dawo min nan ban gama dake ba" ta fad'a tana jawota baya da karfin gaske a fusace Ayrah ta juyo tana fisgewa tace "karki sake zagin mahaifana" jin abinda tace yasa Abidah zaro ido waje cike da tsananin mamaki ta bud'e baki da hanci tana kallon ta tace. "Me naji kince maimaita kalmar da kika fad'a dan inaga kunne nane baiji sosai ba"? A masife Ayrah tace "nace karki kuskura ki sake zagin mahaifana kin gane"? wani irin kallon baki da hankali Abidah tai mata tana cewa "au karna sake zagin mahaifanki humm lallai idan na sake zagin sufa me zaki iyayi zaki dake nine"? Kai Ayrah ta jinjina tana cewa "kwarai zan miki abinda baki ta'ba tunani ba idan kin isa ki maimaita wallahi yau ko Umma zata kashe ni a gidan nan saina fasa miki baki" "Ni zaki fasawa baki"? Abidah ta fad'a tana nuna kanta taga kodai mafarki take cikin 'kwarin gwiwa Ayrah tace "kwarai ma kuwa shashasha haka nace ko kina ganin nayi 'karya ne bazan iya ba"? Cikin 'karaji Abidah tace "eh 'karya kike wallahi 'karya ne abinda kika fad'a amma tunda kince zaki iya bismilllah zoki fasa min bakin d'in nagani" gyara tsaiwa Ayrah tai tana cewa "ok yau kuwa zan gwada miki wace Ayrah a gidan nan idan kin isa kije ki saita min bakin naki a jikin bango ki gani idan ban gurje shiba" kallon tsaf Abidah tai mata tana cizon yatsa ji take inama Nadiya tana nan yau su taru su karya Ayrah ku faffasa mata jiki................. "Ko baki shirya ba na tafi harkar gabana nace kije ki saita min bakin naki a jikin bango ki gani idan ban gurjeshi yai jini ba" maganar Ayrah ta dawo da ita daga maganar zucin da take wani mugun kallo Abidah tai mata har zuciya ta debeta ta sha'ki wuyan Ayrah ta rufeta da duka sai kuma tace bari dai ta taje jikin bangon taga gudun ruwan Ayran da gaske zata iya abinda ta fad'a ko korarin banza ne 'kwafa Abidah taja tana wucewa taje jikin bango tana cewa "zoki gurje min d'in" ta fad'a a fusace tana kallon Ayrah wacce ta karaso itama tana kallonta fuska a tamke tace "ki saita min bakin naki a jikin bangon nace yanzun nan kiga aiki da cikawa yau zan nuna miki kalata duk zaman da muke daku na zuba muku ido ne yau zan fara gwada miki Nima ba kanwar lasa bace bani da dad'i fad'awa a rijiyar fetur d'in da take cida wuta yafi sau'ki akan shiga gonata". Murmushi Abidah tai tana jinjina kai tare da fashewa da dariya tana nuna Ayrah tace "kalleta da Allah sakaryar kawai wato kenan yanzu zaki iya abinda kika fad'a idan na saita miki bakin nawa"?. "Ai magana da cacar baki bazata wadace muba kawai ki saita min bakin kiga yadda zanyi idan zan iya idan ma bazan iya ba zaki gani". Juyawa Abidah tai tana cewa "ok gashi zoki gurje" ta fad'a tana juya fuskarta ta saita mata bakin a jikin bango kamar yadda tace zuciyar Ayrah ta riga ta hangulo da abinda Abidan take mata tana ganin ta samu dama tasa hannu ta dam'ki wuyan Abidan wacce ta d'auka fad'a kawai Ayran take bazata iya mata komai ba saida taji ta danna kan nata a jikin bangon ta fara gogawa da 'karfi Abidah ta d'auka Ayrah bazata iya bafa humm saida taji azaba zata kasheta batasan lokacin data fara ihu ba tana kiran Hajiya Khubura khaleel dake zaune dariya yake harda ri'ke ciki yana hautsinawa akan kujera ganin Hajiya Khubura ta fito da gudu yasa ya mi'ke shima da gudu ya karasa inda suke saboda yasan idan ya bari Hajiya Khubura saita daki Ayrah yana zuwa ya janta yana 6oyeta a bayansa kamar ba shine ya gama dariya yanzu ba ya hade ransa ganin yadda Hajiya Khubura ta susuce ta karad'e gurin da salati ganin yadda bakin Abidah ya fashe yana fitar da jini ta kalli Ayrah dake bayan khaleel tana cewa. "Mitsiyaciya bankad'addiya kashe min 'yar zakiyi kiga yadda kika fasa mata baki har wannan jinin yake ambaliya haka kamar an yanka rago wallahi yau saikin shiga uku a gidan nan" ta fad'a tana juyawa kan Abidah dake kukan azaba da rad'ad'in da bakinta yake mata tana cewa "kema ubanki kika tsaya kallo har wannan figaggiyar ta iya danne miki kai a jikin bango tana gurzawa kamar tana gurza kayan wanki kina tsaye so'ko'ko ya 'kawar bora harta fitar miki da irin wannan jinin tabd'ijan aiko yau idan baki mata dukan mutuwa ba sai naci ubanki a gidan nan" jin abinda Hajiya Khubura ta fad'a yasa khaleel yace. "Wallahi Umma bata isa ta daketa ba meyasa tace taxo ta gurje Mata bakin ita kuwa ta nuna mata isar tata a fili yanzu da taci ubanta gaba zatai shakkarta dama kullum suna takura Mata suna matsa mata daga yau ta fara ramawa dan ubanta itama Nadiyan naso ace harda ita akaiwa haka shegun yara yan iska" nunashi Hajiya Khubura keyi da yatsa ranta a 'bace tace. "Khaleel karka sake zagar min yara na akan wannan 'yar ala tsinan dama Kaine me zuga ta kenan saboda Nadiya tayi aure wato ta rama akan Abidah kenan"?. "Ni bance ta rama akan Abidah ba kawai dai ina fad'a muku gaskiyar magana ne kun dad'e kuna cutar mata yanxu kuma lokaci yazo da zata rama wani abin sai gaba ma idan na aureta ta zama matata wallahi ta daina komai kuma ba 'yar aiki zan nemo ba kura ce za'a ramawa aniyarta Abidan ce zata ri'ka mata komai kama daga girki wanki wanke-wanke da share-share harda wanki toilet wallahi duk saita yi mata idan ta nuna taurin kai ko bana nan tace bazatai ba nazo har gabanki nayi mata shegen duka kuma dole taje tai aikin". Khaleel na rufe baki Hajiya Khubura tai masa wani irin kallon ka fara hauka ne tana cewa "au kaine me goyon bayanta shine kana gani tai mata haka dan asara bakai komai ba karshe yanzu ka 6oyeta a bayanka kana fad'ar wani idan ka aureta Abidah ce baiwar wannan yarinyar hum'um wallahi bata isa ba sai naci uwarta yau saina sumar da ita sannan wahala tasa ta farfad'o". "Kinsan Allah Umma bazaku daketa ba saboda banga abinda tai muku ba idan kuma ramawar kike so Abidan tayi to kibarsu ki koma gefe ki zauna ki zuba musu ido aga wanda zaiji jiki a cikinsu" ya fad'a yana dariya saboda yasan Ayrah tafi 'karfin Abidah kawai dai tana ha'kuri ne da danne komai saboda tsoron abinda Hajiya Khuburan zatai mata murmushi yai yana sake kallon Hajiya Khubura data cika tai fam yace "a fara bismilllah ga fili my Baby fito ku had'a damtse kar kiji tsoron kowa ina so ki nunawa Umma da wannan 'yar iskar yarinyar keba abar rainawa bace Umma kun shirya my wife a shirye take jin abinda yake cewa yasa a masife Hajiya Khubura tace bazan zuba musu idon ba da kaina zanci uwarta ba Abidan data rainawa hankalin ce zata rama ba balle ta mayar da ita kamar wata sa'ar ta". "Umma kar kiyi haka dahuwar hankali ayita da ruwa Abidah bata da gaskiya anan bai kamata kice danta tsokani Ayrah ta daketa saikin rama mata ba zan fita amma wallahi na rantse da Allah idan na dawo na tarar kun daketa saina 6allawa wannan yarinyar 'kafarta" ya fad'a yana nuna Abidah sannan ya juya inda Ayrah take tsaye yana kallonta yace "ko kallo Abidah tai miki wanda bai gamshe kiba idan na dawo ki fad'a min zataga yadda ake wasan tsutsa a rana ta sanni tasan halina dan ubanta ba'ai min raini" yana fad'in haka ya juya yama fice daga gidan gabadaya jin tashin motarsa yasa Abidah fashewa da kukan ba'kin ciki tana cewa. "Umma kiji Yaya khaleel da mugunta nufinsa bazan rama ba kenan ta daki banza saboda yana sonta wallahi saina daketa saidai idan ya dawo ya kashe ni" ta fad'a tana tafiya ta gudu ta cafki Ayrah suka hau dambe da sauri Hajiya Khubura taje ta janye Abidan tana cewa "ke dan ubanki ki rufawa kanki asiri kinsan khaleel d'anye ne ba isasshen hankali ne dashi ba zai iyayin abinda yace ki kyaleta kawai akwai ranar ramawa domin bata isa ta fitar miki da jini mu barta taci bulus ba muma saimun fitar mata amma ba yau ba muje" ta karasa maganar tana janta suka bar gurin tsaki Ayrah tai tana wucewa ta shiga bedroom d'inta domin tai wanka tazo taci abinci tasa a ranta itama daga yau bazata sake yarda Abidah tai mata wani abu ta rabu da ita ba ramawa zata ri'ka yi tunda ta fahimci a baya sunyi amfani da damarta yanxu kuma kan mage ya waye itama ta fara gane abinda ya kamata tayi idan sun 6ata mata karta rabu dasu ta d'au mataki da kanta. *•*•* Su Nadiya amarya manya maganin karagar 'kasa yau bari mu le'ka gidanta muga meke faruwa idan ta rage mana kazar amarcin mu gwangwaje😋 tana zaune ta hakimce a parlor anci kwanka Sabit ya fito shima cikin shiri tana ganinsa kuwa ta sake d'aukar sabon salon kissa tana karairaya ta tashi tana rungume shi ta sakar masa kiss tana murmushi tace "wow kayi kyau sosai my one kaga yadda kake wani she'ki kamar gold"? Ta fad'a tana dafe kafad'unsa gira ya d'auke mata yana kallon ta shima yace "da gaske nayi kyau"? Kaita d'aga har lokacin bata daina murmushi ba saboda tana tsananin sonshi tace "da gaske nake har naji kishi ya kamani yadda kayi kyan nan karmu fito 'yan mata su kalle mun kai" ta karasa maganar a shagwa'be tana d'an jada baya harda bubbuga 'kafa jawota jikinsa yai yana cewa "karki damu ki daina damun kanki babu wacce ta isa tai miki 'kwace na domin ina tayaki kishin kaina" yana rufe baki ta saki dariyar farin ciki tana cewa "yauwa alhamdulillahi wallahi har kasa naji dad'i a raina dama nasan kana sona kana jidani shiyasa nima nake kula dakai sosai" ri'keta hannunta yai yana nufar kofar fita harabar gida yace "taho muje kar lokaci ya 'kure mana" janta yai suka fita har zai dau'ko musu motar a rumfar aje motors na gidan Nadiya tace ya barshi yau marmarin tafiyar 'kafa take so tare suka fita hannunsu ri'ke da juna suna tafe suna shan soyayya hummm suna wucewa Boukar dake ra6e ya fito yana d'aga waya da sauri ya kira Mah kamar yadda tace idan ya ganshi ko duk sanda ya samu wata 'yar alama ya kirata ya fad'a mata yana kiran nata kuwa kamar jira take ko wayar na hannunta cikin gaggawa ta d'aga tun baiyi magana ba tace. "Hello Boukar ka ganshi ne"? Kai Boukar ya jinjina yana qara kallon hanyar da suka bi kafin yace "eh na ganshi yanzun nan Mah wallahi da gaske ne abinda ake fad'a domin tunda nazo nake bibiyarsa kamar yadda kika bu'kata kuma na gano gidan da yake zaune tare da matar tasa Sabit yayi aure yanzun nan suka wuce ta gabana amma ban yarda ya ganni ba" daga can 'bangaren matar tace "ok kasan mezai faru yanxu kaci gaba da kula min da motsinsa karka yarda yasan kana garin so nake nazo na ritsa shi da matar tasa naci ubansu tunda ya raina min hankali jira nake Naomi ta karasa exam d'inta mu taho nan d'in tare harda Niseh yanxu inaso ka bisu ka gano ina zasuje". "Ok Mah" ya fad'a yana katse kiran da sauri ya mayar da wayar aljihu yana bin bayansu da gudu tunda yaga ba'a mota suka fita ba yasan bazasu yi masa nisa ba zai tarosu yanzun nan. HUMM MUJE ZUWA🤨. ✍️Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë 🌺. Tnks for ur supports 🔥 yusrah ce. TYPING 📲 Fri April 2025 3:00PM YUSRAH MUSA ABUBAKAR ✨💯. 👑 ROYALTY 👑 ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫 Gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan ta. STORY WRITTEN ND EDITING ✍️ YUSRAH MUSA ABUBAKAR Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë. 🕋🕌🕋 It's Friday don't forget to recite suratul al-khaf may Allah bless us may Allah open the door of success to us may Allah forgive us may Allah protect us and our family from all calamities Amin. 14~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Muttaqinah. @YUSRAHMS CE Page 27 & 28 Su Khairat basu san yau Ahmad zai koma ba harya shirya basu shigo part d'in ba suna part d'in Mami saida ya kira wayar Khairat yace yanxun nan su sameshi a gurin Momy kafin ya kirga goma karta kashe wayar zai ri'ka kirgawa suna ji hmm da gudu suka shigo kowa tana haki ganinsa cikin shiri yasa suka zaro ido waje suna kallon juna oh ashe tafiya zaiyi tome sukai masa yake nemansu ko dukan bankwana zai musu domin Kiran dayai ma sun d'auka laifi sukai masa saida suka zo suka ganshi a haka tuni kowa taji zuciyarta wasai da sauri suka karaso suna zuwa gabansa ya kallesu yana cewa "baku iya gaisuwa ba"? Tuni suka nutsu suna daidaita numfashi sukace "ina kwana''? Bai amsa ba sai kallo da yake 'kare musu daga baya yace. "Ummul-khairi da Zuhra Allah ya kawo mu yau zan tafi zan barku sai ranku yai fari mugu zai koma inda ya fito amma ku sani na tafi ina nan haka nake kuma zaku gani ban baku ha'kuri ba idan bana nan dan Allah kar kuyi abinda nace ku 'ketare sharud'an dan saka muku Ina daidai daku" juyawa yai yana kallon Momy wacce ta girgiza tana murmushi yace "Momy ki zama witness na riga na fad'a musu komai kar tsautsayi yasa su aikata min zan hukunta su suce kuskure ne ko Abdul-Hamid ya shiga maganar please Momy dan Allah duk abinda sukai ba daidai ba idan na kiraki ki ri'ka fad'a min zan rubuta a littafi na aje sai ranar dana dawo idan laifi d'ari sukai saina hukunta su sau d'ari bazan gaji ba idan suna bukata harda 'kari zanyi musu". Kai Momy ta d'aga tana cewa "Karka damu Ahmad insha Allahu bazasu kuskure ba zan lura dasu kasan su waye 'kannan ka akwai tarbiyya da ladabi ko baka bada sa'kon a kula dasu ba bazasu aikata maka kuskure kamar yadda ka hanesu ba" Momy tana rufe baki ya mayar da hankalinsa kansu yana jinjina kai yace "ba kunji ta shedeku ba wallahi idan naga abu sa6anin fahimta sai naci uban ku" ya fad'a fuska a d'aure ba wasa kafin ya mi'ke yana kallon Momy da itama ta mi'ke tana cewa "muje nayi maka rakiya Allah ya kiyaye hanya Allah ya dawo min dakai lafiya" da sauri Maryam da taci wanka tad'au kwalliya itama ta taso tana taku tazo har gabansa da karairaya tana sauya murya ta ma'kaleta sosai tana cewa. "Nima fa Ahmad yau harda ni za'ai maka rakiya tunsa Allah yasa ina gidan yau sai munje har airport tare sai naga tashinka koda ace zan baro can" bai kalleta ba kuma baiyi magana ba sai hanyar fita daya nufa Momy kuma ta koma part d'inta zata d'auko hijab da kallo Maryam ta bishi tana cije lips ji take kamar ta sake kiran sunansa amma bakinta yayi nauyi kawai kwarjini taga yayi mata musamman yau data sake ganinsa cikin kakin soja sai ta sake jin wani irin bala'in sonsa da kaunarsa suna linkuwa suna shiga zuciyarta gashi jinin sarauta gashi soja ga kyau da kud'i da ilmi innalillahi wa inna ilaihi raji'un ya Allah ka duba al'amari na ka bani bawan nan naka matsayin miji a gareni" ta fad'a a ranta tana sake kallon kofar daya fita wayar Khairat ya kira yace su fito waje yana jiransu ganin sun fita yasa Maryam bin bayansu da sauri kamar zata kifa tana cewa "ji wani rainin hankali wato saboda ni banza ce ka shareni amma su saida ka fita ka kirasu a waya su bika to wallahi ko har Russia zasu rakaka nima sai naje babu wanda ya isa ya hanani" ta fad'a da gudu ta fita itama daga part d'in Mami ta ganshi ya fito tare da Mami itama tana yi masa kyakkyawar addu'a har gaban mota sukaje prince Hamid zai kaishi duk suna tsaye bayan ya shiga ya zauna kusa da prince Hamid ya kalli su Khairat da suke tsaye suna 6oyewa a bayan Momy yace ''kai me kuke jira ku shiga back seat ko baku gane bane"? Zaro ido sukai Ina yake nufin zasu rakashi har airport ko kuma ina yake cewa su shigo............. Katse musu tunani yayi da cewa "Dan ubanku baza kuyi min rakiya ba zan tafi shine kuka zuro min ido kuna kallona wato yauma farin ciki kuke zan koma na dad'e ko"? Dariya prince Hamid yai yana cewa "kai malam ba'a son mugunta ina zasu rakaka ka 'kyale yaran nan su sha'ki iska mai kyau dan Allah". "Wallahi bazan kyale suba sai sunje" ya fad'a yana sake kallonsu murya ba wasa yace "zaku shigo ko saina fito kanku"? Tun bai rufe baki ba suka bud'e suna shigo kowa salati take bud'ewa itama Maryam tai tana shiga ta zauna kusa da Baby harda sake turata tana matsar ta dan tai magana ita kuma ta share kamar batasan da wanzuwar Maryam d'in a gurin ba hakan kuwa yasa ciwo a ran Maryam badan da Ahmad a motar nan ba wallahi yau saita faffalwa Baby maruka da zuciyarta tai sanyi................. Jin mota ta tsaya yasa ta d'ago daga tunanin da take tana kallon gurin a ranta tana cewa "to ina ne nan kuma dama ba airport zaije ba"? Ganin sun fito suna shiga yasa itama ta fito tana bin bayansu batasan gurin kakaninsu suka zo ba saida ta shigo ta gansu kan bala'i dama kakaninsu suna nan a raye bata sani ba anan suke a cikin masarautar kodan suna 6angaren su daban ne shiyasa basa zuwa kuma da nisa humm aiko taga gurin zuwa dole ta ri'ka kawo musu ziyara saboda su saba zata ri'ka nuna musu tana son Ahmad ko Allah zaisa ta dace tunda taga acan bata samu kar6uwa a gurin Momy ba. Iya su kadai suke zancen su banda ita saboda batasan me zatace ba kusan awarsu guda anan sannan suka mi'ke suna yi musu sallama suka fita su Baby kam sunyi tunanin iya nan zasu rakoshi shiyasa da suka fito iya Maryam ce ta shiga motar sukam daba marmarin tafiya tare dashi suke ba babu wacce tai motsi saida suka ji yace "ba iya nan zaku tsaya ba har airport zamuje mun fito kun wani 'kame a gu d'aya kamar dogarai ku shigo man kuna 6ata min lokaci" ya fad'a harda zare musu ido ba shiri sukai kowa tai 'kasa dakai saboda tsoron karma su had'a ido yace wani abu ko yace sun masa laifi tunda sun fahimci so yake yad'an ta'ba lafiyar jikinsu Kuma badama domin babu wanda yai masa laifin dazai dake sun shiyasa yake jansu kafin aje airport d'in ko zasuyi masa laifin.......... "Baby da Khairat baku ji abinda nace bane"? Kai Baby ta girgiza tana cewa "kayi hakuri Yaya ni kaina ke ciwo" ta karasa maganar har lokacin kanta yana 'kasa taki d'agowa gudun karya gane karya take son zuwa airport din ne batai...... "Ko duk jikinki ne yake ciwo yau sai kinje airport d'in nan wallahi tunda na rantse ba kaffara shigo" wata iriyar harara Maryam ta sakarwa Baby tana gyara zama ta babbake gurin dan karsu shigo tana kallon Ahmad ta mirron mota tace "kaima Ahmad kamar dole saida su mezasu baka daka damu saitaje tunda tace kanta ke ciwo ka kyaleta man su koma tare da Khairat ni zanyi maka rakiyar har airport d'in ma dawo tare da Abdul-Hamid" bai kula maganar da Maryam ke masa ba sai kallonsu dayai yana cewa "wai uwar me kuka tsaya kallo na fito kenan"? Ya fad'a yana shirin bud'e murfin motar ya fito ganin da gaske yake yasa da sauri kowa ta bud'a ta shiga kaiya jinjina yana had'e fuska daidai prince Hamid ya tada mota ya kalleshi da murmushi yana cewa "Allah ya shirye ka kai dasu kamar wasu Tom and Jerry kaine Tom d'in su kuma Jerry's ace ba dama ku kasance guri d'aya bakinka bazai shiru ba ka d'an ri'ka d'auke kai mana". "Wallahi basu isa ba indai suka samu damata kamar yadda suka samu taka humm wadannan yaran" ya fad'a yana nunasu ta mirror yana cigaba "da babu wanda zai fad'a musu suji kana gani fa wancan lokacin ina barin gari suka d'aura balloons harda sayo cake wai sukai valentine na tafiya ta kodan harda kai aciki laifinka ne daka hanasu baza suyi ba" Ahmad na rufe baki prince Hamid ya girgiza kai yana cewa "a'a malam kada ka la'ka min laifin daba nawa ba ni bansan party zasuyi ba wallahi har suka gama shirinsu saida na shigo gurin Momy zan gaidar da ita da la'asar sannan naga suna had'awa na tsaya na kalla kaga kuwa mene laifina a cikin nan waye me laifi d'an kallo ko me aikin"? Baki Baby ta rufe tana kallon Khairat wacce itama ta zaro ido ganin prince Hamid yana neman ya tada mutuwa daga barci yasa Ahmad ya dawo da laifin sabo yadda suke a airport d'in nan ba kusa da Momy ba ya dagargaje su son ransa, sun d'auka Ahmad zaiyi magana da prince Hamid yace haka sai kuma sukaga baice komai ba babu wacce batace alhamdulillahi a zuciyarta ba sai Maryam da take cika da batsewa ita kad'ai ganin kamar duk sun manta da ita a cikin motar d'an karamin tsaki taja wanda bai fito fili ba daidai sun shiga airport d'in prince Hamid yayi parking suna fitowa yana cewa. "Ahmad wannan lokaci ma yaso fita fa"? Ya fad'a yana kallon agogon hannunsa tsaye Ahmad yai a gurin yana mi'kawa prince Hamid hannu sukai musabaha yace "please Abdul-Hamid dan Allah na baka amanar kula da yaran nan duk abinda sukai kuskure karka 6oye min ka kirani ka fad'a min dan Allah saboda tunda suka fara idan na tafi su had'a party bazasu daina ba sunyi d'aya kar suyi na biyu idan suka sake zasu had'u da fushina wanda sai sun gwammace dama basu zo duniya ba" ya fad'a da serious face yana kallon su ganin yadda duk suke a tsarake kamar masu shirin zubawa da gudu jinjina kai prince Hamid yai yana cewa. "Karka damu Ahmad insha Allahu ni nayi maka alkawari bazasu sake aikata hakan ba idan baka nan" ya fad'a yana jijjiga hannunsa da yake ri'ke dana Ahmad d'in "ok thank so much zanso hakan ya faru na tafi saina dawo" ya rufe baki Maryam har 'kwaruwa tai wajen cewa "please Ahmad dan Allah ka tsaya Abdul-Hamid yayi mana photo" kamar bazai amsa mata ba sai kuma ya juyo yana kallonta kamar me nazari kashe masa ido tana matsowa inda yake cike da iyayi ta mi'kawa prince Hamid waya fuskarta fal da murmushi kamar an biya mata hajji tace "yauwa dan Allah d'auke mu Abdul-Hamid d'auke mu" ta fad'a tana sake mannuwa a jikin Ahmad d'in ganin yau ta samu damar data dad'e tana so har kwantar da kanta a jikinsa take tana qara matsarsa duk yana jinta yana shan kallonta kawai ya shareta ne shima saboda ganin tafiya zaiyi bai kamata ace sunyi rabuwar wula'kanci ba kusan photo ashirin akai musu kafin Ahmad yace ya isa haka kar'bar wayarta Maryam tai daga hannun prince Hamid tana dubawa jikinta har rawa yake tsabar yanayin data tsinci kanta na jin dad'i da shau'kin yau tayi photo tare da Ahmad ta ta'ba jikinsa humm har lokacin ji take kamar tana jikin nasa basu rabu ba. "Kun tsaya kallo nane ku baza kuzo muyi photon ba saboda bakwa son gani na ko kun matsu na tafi ku daina ganina haka ne"? Da sauri suka girgiza kai a tare suna cewa "a'a Yaya kayi ha'kuri" dariya prince Hamid yai yana kallon su yace "wato harda had'a baki kukai a bada ha'kurin idan ma photon ne dashi bakwa so mene a ciki ana dolene". "Ok Kaine kake zugasu kenan"?. "Ni ba nine nake zugasu ba kar kayi wannan zargin kawai dai na fad'i hakan ne saboda Naga kana neman takura musu idan Kuma basu da ra'ayi fa saika 'kyale su". "Wallahi sai an d'auka harda wani had'a baki suna bani ha'kuri kamar wasu 'kadangaru suna girgiza min kawuna zaku zo muyi ne ko saina................. Tun basuji hukuncin dazai yanke musu da gudu suka karasa inda yake tsaye kallon Khairat yai yana cewa "ke tsaya anan" ya nuna mata 6angarensa na hagu sannan Baby 6angaren hannun dama ya baiwa prince Hamid wayarsa yayi musu kar'ba yai yana dubawa ganin babu me fara'a a fuskarta ya d'ago ya kallesu yana cewa "bakwa so mukai photon nan babu wacce fuskarta da murmushi kamar wanda kuka samu mummunan labari kuzo ya sake mana wani duk wacce batai murmushi ba tare zamu tafi muje can naci ubanta sannan na sakota a jirgi ta dawo gida idan na dawo kuma tai watering"😳 jin abinda yace yasa kowacce ta sake fuska a bisa dole sukai murmushin da basu shirya ba har saida suka saka prince Hamid dariyar dabai shirya ba ya kalli Ahmad yana cewa. "Ahmad ka zama mala'ikan yaran nan tsoronka da suke ya 6aci please ka rage wasu abubuwan kodan gaba Ina fad'a maka haka kullum ka'ki wallahi abun zai dameka fa" Ahmad baiyi magana ba sai wayarsa daya kar'ba yana kallon prince Hamid yai mai magana da ido kaiya jinjina suna shirin wucewa yace "ya kamata nima ace munyi photon nan kafin ka tafi Ähmäd" jin abinda ya fad'a yasa Ahmad dakatawa yana bashi wayar alarmar yayi musu kar'ba prince Hamid yai yana mi'kawa Maryam wacce da sauri ta kar'ba ganin wayar Ahmad ce to d'auka iya su biyun zata d'auka sai taga Ahmad yasa su Baby su shigo tuni ta tsuke fuska tana sau'ke wayar kasa ta kalli prince Hamid tana cewa. "Ya haka ba photo kace zanyi muku kai dashi ba"? Kaiya d'aga yana cewa "eh man d'auke mu sauri yake zai wuce lokaci ya cika" 'kara had'e rai tayi tana cewa "ok su fita gefe nayi muku zakufi kyau ku biyu". "Su waye zasu fita"?. "Su Khairat idan sun shiga zasu 6ata muku photo" ta fada kanta tsaye tana harare-harare da mamaki prince Hamid yace "akan me zasu fita taya zasu 6ata mana photo"?. "Ta yadda ake 6atawa kalli ma basu dace ku d'auka dasu ba nidai badasu zan d'auka ba kaine ka bu'kaci ayi muku photo kaga kuwa ai banda su ko"?. "No harda su wannan na family dukkan mu zamuyi saboda tunawa kin gane"? Jin abinda yace yasa Maryam tace "oh indai photon family ne saidai mu nemi wani yayi mana tunda nima ba bare bace bari naiwa wani magana" tana rufe baki Ahmad yace "give me my phone" ya fad'a yana mi'ka mata hannu bata bashi ba sai baya kad'an data matsa tana cewa "akan me zan baka ka bari man ga wani ya taho ya d'auke mu kodan nace haka shine zaka 'kwace gani nayi nima jininku ce akan me za'a wareni"? Jin abinda take cewa yasa Ahmad yai banza da ita ko karasa kallonta baiyi ba sai prince Hamid da yace. "kina jiko Maryam ki fahimta ba hakan yana nufin za'a wareki bane a'a photo ne zamuyi na family 6angaren gidan mu d'aya ba dangi ba shiyasa ba'a saka dake ba ke kina 6angaren Momy ne basu abbanmu ba amma idan mun 6ata miki ranki akan hakan kiyi mana afuw................. "Abdul-Hamid" Ahmad ya fad'a muryarsa da alamar fushi kallonsa prince Hamid yai ganin yadda ransa ya 6aci akan maganar da Maryan ta fad'a yasa ya mayar da hankalinsa kan Maryam d'in yana cewa "bani wayar lokacinsa yana neman fita" mi'ko masa tai shi kuma ya mi'kawa Ahmad kafin suka wuce saida ya rakashi har gaban matakalar jirgin ya shiga sannan ya juyo ya dawo gurin da suke tsaye sai iya Baby da Khairat ba Maryam a gurin. "Ina Maryam ta tafi kuma"? Ya tambaya yana kallonsu Khairat ce ta bashi amsa "tana cikin mota Kuna tafiya ta koma" ok muje" ya fad'a suna wucewa tana zaune a gidan gaba tana kallon photunan da prince Hamid yai musu yanzu ita da Ahmad sai status take dasu tana turawa a group din'ta tana fad'awa 'kawayen shine mijin da zata aura tajin sanda suka shigo motar bayan tafiyar ahmad babu wanda ta d'ago ta kalla har ya tada mota suka tafi iya su uku suke magana a motar amma banda ita har dariya prince Hamid yake ganin yadda suka ware suna hira dashi amma d'azu sakamakon da Ähmäd motar ko tari babu wacce take yi sai iya Maryam. Suna zuwa gida ko tsayawar minti d'aya Maryam bata sake yiba kai tsaye ta wuce bedroom ta d'auko jakarta tana fitowa Momy dake zaune tare dasu Khairat suna fad'a mata abinda ya faru da Ahmad yasa dole suyi masa rakiya kawai sai ganin Maryam sukai ta bud'o kofa ta fito zata tafi da mamaki duk suka bita da kallo Momy dake kallon yadda Maryam d'in take kumbure-kumbure tace. "Maryam ya haka ina zuwa kuma"? Murya 'kar-'kar alamar tana cikin fushi tace "gida zan tafi" da mamaki Momy tace "gida dai? Haba Maryam rana tsaka kice zaki tafi gida babu shiri ba komai dama haka ake zuwa ziyarar"? Shiru Maryam tai Momy taci gaba "babu inda zakije saikin dad'a yimin sati a gidan nan koma ki aje jakar nan yanzu ki dawo nan muyi hirar tare" jin abinda Momy tace yasa Maryam kamar zata fashe da kuka tace "dan Allah Momy ki barni na tafi wallahi zan sake dawo muku yanzun uzuri ne ya taso min". "Wanne irin uzuri kuma ko a school"? Kaita girgiza tana cewa "a'a ba'a school bane gida zanje gurin Mama" murmushi Momy tai tana kallonta kamar zata sake cewa wani abu sai kuma ta 'kyale tana cewa "ok ki gaishe min da ita nagode sosai da ziyara Allah yayi miki albarka" su Khairat ta kalla tana cewa "ku tashi ku d'an taka mata man" Momy ta rufe baki Maryam ta girgiza kai da sauri tace "a'a basai sun rakani ba suyi zamansu na tafi" ta fad'a fuuu tana nufar hanyar fita dakatar da ita Momy tai. "Amma ai kya tsaya Khairat ta taso taiwa driver magana ya kaiki ko"? Nan kaita girgiza a karo na biyu tace "a'a Momy nagode zan fita can waje bakin titi na tari d'an napep saina sake zuwa miki" tana fad'in haka ta bud'e kofa wuff ta fice murmushi me had'e da jinjina kai Momy tai tana mi'kewa ta shiga part d'inta ta d'auko kud'i tana baiwa Khairat tace "tashi maza yanzun nan ku kai Mata tahau napep d'in ko ta'ki kar'ba karku dawo min dashi kusan yadda zakuyi ku bata" kar'bar kud'in Khairat tai suka mi'ke tare Baby suka bi bayanta tsabar saurin da take harta fice daga masarautar sai acan wajen gate d'in karshe ma farkon shigowa suka sameta hakan ma sai kira Khairat ta 'kwalla mata tana ji tai banza har saida suka dad'a sauri suka tarota kud'in Khairat ta mi'ka mata tana cewa "gashi Momy tace kihau napep ya kaiki gida" baki Maryam ta ta'be tana girgiza kai tace. "No nagode ki maida mata kud'inta ina dashi kud'in da yake gurina ya isheni har yayi min yawa". Kallon yadda ranta yake a 6ace Khairat Tai tana cewa "Tace karna mayar mata matsayin naki dabam nata dabam please Maryam ki kar'ba". "Nace miki a'a ki mayar mata ina da kud'in zuwa gida ya ishe ni". "Amma a tunani na Maryam ko duniya ce a tare dake dan Momy ta baki kud'i ki hau abun hawa bai kamata kice a'a ba ra'ayi tai ta baki aitasan kina da kud'in ta baki ki kar'ba dan Allah". "Khairat kinsan halina fa idan na riga na furta abu na furta kenan bana canzawa nima yakamata ki fahimce ni nace miki na gode ki maida mata ko bakiji sosai bane"? Ta fad'a tana aikawa Baby harara da dogon tsaki wacce tunda suke maganar su ko tari batai ba sai yanzu Maryam take nemanta da fitina tace "ke kuma uwar zulai meye kika zuro min ido kina min kallon 'kurulla idan make me lashe-lashe ce toni nafi 'karfin ki saidai kici kanki gida da bedroom kuma gashi na bar miki ki dafa kici nima muna da arzikinsa ba fatara ce ta kawoni gidan naku ba balle kiyi min wani jakin kallon ki" jin abinda Maryam tace yasa Khairat tai mugun had'e rai tana cewa. "Wai Maryam wanne irin abune wannan kike yi yada girman yayi yawa dan masifa bata kulaki bama saikin takale ta kunyi fad'a dad'in abun ma ita wacce kikeyi dan ita ko kallo baki isheta ba kotanan ya kamata ki sallama kiyi Dana sani nadama da saranda akan abubuwan da kike ba daidai bane" zazzafar harara Maryam ta sakar wa Khairat tana cewa "Babu ruwanki ba dake nakeyi ba gada wacce nake maganata idan ta isa yau ta tanka min kamar yadda Tai min kwanan baya wallahi saina 6allata a gurin nan dama ina wuya da ita dan haka duk abinda zamuyi naki idone Khairat karki shiga abinda ba'a saka dake ba karki d'auka" ta fada tana mayar da kallonta kan Baby tace. "Ke kuma ina sauraron ki idan kin isa ke cikakkiyar fitsararriya ce kiyi min magana yanzu kiga aiki da cikawa" d'auke kai Baby tayi tai banza da ita kamar dai irin bada ita take ba takaici ne ya kama Maryam har batasan lokacin data ciji yatsa ba murmushi Khairat tai tana cewa ''nida nasani Baby bazata kulaki ba ko kanki zaki cinye saidai kici ke kad'ai gashi kuwa hakan ya tabbata kinga da zaki gane saiki daina wahalar da kanki a kanta dan indai ba rashin neman zaman lafiya ba banga abinda ta tare miki ba alhali kece kika zo kika sameta". "Ai dama bazaki ga abinda tai min ba saina fad'a amma ki sani bani da lokacin ku dukka biyun baku isheni kallo ba banzaye ku jira dawowa gidan sai nayi maganinku mtswww" taja tsaki a fusace tai gaba da kallo Khairat ta bita tana cewa "Allah ya yaye miki wannan abubuwan idan masifa ce ta sameki idan kuma zaki gyara Allah ya ganar dake da wuri muje Baby" juyawa sukai suna komawa Momy tana zaune a inda suka barta basu nuna bata kar'bi kud'in ba ko kuma ga abinda tai kawai Khairat tacewa Baby kar tace Maryam ta'ki kar'bar kud'in sun dawo dashi zata 6oye sai abun ya wuce yadda koda ta fito da kud'in nan tace mata bata kar'ba ba tasan sannan abun bazai mata ciwo kamar yanxu ba shiyasa ma fuskarsu wasai suka dawo mata suna d'ora hirarsu daga inda suka tsaya. Maryam kam me napep ta d'auka har kofar gate d'insu ta bashi kud'insa tana d'aukar kayanta ta shiga ciki Mama tana zaune a parlor sai ganinta Tai ta shigo mata kamar mafarki harda murje ido Tai ganin da gaske itance yasa zubur ta mi'ke tana tahowa gurinta da sauri tace "Maryam ya na ganki haka da rana tsaka meya faru dawowar me kikai ne kardai wani abu ne ya faru a tsakanin ku"? Zama Maryam tai tana sau'ke numfashi tace "a'a kwantar da hankalinki babu abinda ya faru kawai tahowar dad'i ne". "To kice yau da labari kenan mu bud'e kunnen mu dakyau"? Kai Maryam ta jinjina tana cewa "akwai Mama labari d'aya kenan saidai kice akwai labarai". "Tofa labarai humn a fad'a mana muji dan harna 'kagu sosai naji abinda yake faruwa" ta fad'a tana sake matsowa ta saito kunnenta dariya Maryam tai tana cewa "kai Mama akwai son jin labari dama ba wani abu bane ya sakani farin ciki sai photo da mukai da Ahmad d'azu" zabura Mama tai tana kallon ta tace "um um fa Maryam banda 'karya Ahmad d'in nan a yadda kike fad'a min baya ko kallonki shine zai yarda kuyi photo"? Murmushi Maryam tai tana d'auko wayarta a cikin handbag d'inta ta bud'e tana nunawa Mama wacce babu kunya ta mike tana rawa harda wa'ka a gaban maryam d'in saida ta gama ta tsaya ta kalli Maryam tana zama tace. "Yauwa Masha Allah sai mene ya faru"?. "Babu komai kawai sai rakiya da mukai masa zuwa airport ya koma Russia shiyasa na tattara kayana na dawo gida kinsan yanzu zan taho harna fito sosai wai sai sannan Momy ta turo Khairat wai ga kud'i nahau napep ni kuwa na'ki kar'ba nace ta mayar mata dan tasan naji haushi" harararta Mama tai tana cewa "ji banza kawai meye abun 'kin kar'ba raba arne da makami ibada ne kikasan nawa ta baki" shiru Maryam tai tana d'aga kai sama kamar me tunani tace"kuma fa da yawa kud'in nan Naga suna da tudu yakai kusan dubu............... "Ke rufe min baki bana son kayan haushi kawai fad'a min meya faru a gidan tun daga ranar da kika je har zuwa yau yanzun nan da muke magana yaya kukai da Ahmad shin kin samu shiga ne koko a'a"?. Kai Maryam ta girgiza tana cewa "humm wai babban aiki kenan gaskiya yanxu a gajiye nake zanje na huta idan na fito saina fad'a miki komai nidai kawai abinda zai Dade yana bani mamaki shine yarda da Ahmad yai ya tsaya mukai photo kawai hakan ne yake 'kayatar dani". "A ina kukai photon ne a gidansu"?. "A'a airport fa mukai masa rakiya". "Ok komawa yai kenan shiyasa kika taho"?. "Uhm ya tafi d'azu sai kuma ya dawo amma naga tunda nazo nace miki ya koma" gyara zama Mama tana d'aga kai alamar eh sannan ta kalli Maryam da fuskarta take fitar da annuri na annashuwar wannan maganar da suke tace "ke Maryam baki fad'a min ya kukai dashi meya faru da kikaje gidan yaya kinyi kokari ya fahimci kina sonsa ne ko a'a a sadaka kikaje yanzu kika dawo min gida a alakoro"? Kai Maryam ta girgiza tana cewa "eh to gaskiya ban sani ba koya fahimta domin shi murd'add'an mutum ne baka iya ganewa inda ya dosa zai iya idan ya fahimci ina son nasa ma ya shareni sai daga baya ya furta min nidai haka nake tunani Dan komadai mene na tabbata yasan ina sonsa tunda kunyi magana da Momy kuma ai nasan ta fad'a masa duk da har yanxu bakiji amsa ba a bakin Momyn zata fad'a miki idan ya fad'a mata itama fa tana so ya aureni dan ta fad'a min cewa na kwantar da hankalina Ahmad zai aureni shiyasa ba na sharesa nasan ko ya'ki da tasa baki shikenan an wuce gurin ko"? Ta karasa maganar tana kallon Mama wacce tunda ta fara magana take jinjina kai tana murmushi har takai aya kafin ta d'aga hannu sama tana cewa. "Alhamdulillah Allah nagode maka ubangiji ka tabbatar min da abun nan ya Allah kasa Maryam tana rabon auren Ahmad a rayuwa wannan shine burina ubangijin rahma ka cika shi" Karki damu Mama ki manta da batun aure kam nida Ahmad a rubuce yake saina aureshi domin bazanyi dakon sonshi a banza ba kuma ina kallo ya auri wata a gabana tabd'i wallahi hakan bazai ta'ba yuwuwa ba never in history har abada inko wata tai gigin shiga hurumin daba nata ba zataga hauka da bala'i saina kasheta". "Daina ma 6ata bakinki da kiran mutuwa ba wannan maganar kawai dai bazamu amince ya auri wata ya barki ba wannan shine Kat idan kuma yaji a ransa shi da akwai wacce yake so ko yake son aura saiya had'aku biyu nan ma na gamsu amma ban amince da ace ya watsar dake ya auro wata tsinanniya shashashar ta zauna dashi ba ita kad'ai ba". Mi'kewa Maryam tai tana cewa "bari na karasa ciki Mama idan na fito xanyi miki bayani dalla-dalla yadda zaki fahimce ni domin nima yanzu ba daidai nake jina ba" da kallo Mama ta bita tana murmushi tace "ok Maryam ina jiranki dan bazan iya moruwa ba sai naji yadda kukai dashi Allah yasa dai kinyi nasara" ta fad'a tana sake kallon kofar da Maryam d'in ta shiga kafin itama ta mi'ke tana shiga bedroom nan da awa d'aya ta fito koda maryam bata fito ba ita zataje har part d'in nasu ta fito da ita yau sai taji labarin nan da hankalinta ya kwanta...........✍️ Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë🌺. See you tomorrow morning at 8:56am insha Allahu. Nagode da kulawa masoya godiya sosai sosai godiya🤝. YMA DUTSE NEW WORLD 🌏 √√√√√√√√√√√√√√√√√√√√√√√ TYPING 📲Sat Apr5/25 02:49pm YUSRAH MUSA ABUBAKAR ✨💯. 👑 ROYALTY 👑 💫A*W*A💫 ••••ANNURI ••••••✍️WRITER'S ••••••••••ASSOCIATION STORY WRITTEN ND EDITING YUSRAH MUSA ABUBAKAR ✍️Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë. 15~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Mustagfirinah. @YUSRAHMS CE. Page 29 & 30. Rashin waya a hannun Ayrah ba karamar illah bace gashi babu yadda za'ai taje gidansu Aiman tai waya dashi ko a wayar 'kannansa tunda Daddy yayi mata iyaka da gidan Baby kuma ba wayace da itaba balle idan tazo school ta ara tai kira sosai tai mugun shiga damuwa wanda har damuwar tata bata 6oyuwa koda school taje bata tsayawa tai karatu sosai yanzu har saida Baby ta tambaye ta mene matsalarta ta fad'a mata ganin cewa itama bazata iya yi mata maganin matsalar ba tayi kokari ta rarrasheta sannan tace idan prince Hamid yazo d'aukarta anjima zatai masa magana ya bata aron wayarsa tunda tace ta ri'ke numbar Aiman d'in a kanta ta saka tai kiransa koma mene ta fad'a masa ya d'auka mata mataki. Da yake yau dogon lecture ne har 'karfe biyar da rabi suna school sai wajen shida suka tashi sakamakon Baby tacewa Ayrah ta jira prince Hamid yazo ta amsar mata wayarsa tai kiran Aiman shiyasa bata tafi ba suka fito tare a tsaye jikin mota suka sameshi yana jiran fitowar Babyn karasawa sukai Ayrah na gaidashi cikin sakin fuska ya amsa mata domin yawan zuwa d'aukar Baby da yake yanzu yasa ya santa sosai kallon Baby yai wacce gabadaya hankalinta ke kan Ayrah yace. "Baby yaufa 'kurarran lokaci ne kafin muje gida za'a kira sallah har yaushe naje nayi alwala bana so na rasa jam'i ko akwai abinda kike bu'kata ne naga fuskarki kamar da alamun damuwa"? Kai Baby ta d'aga ranta babu dad'i musamman yadda taga Ayran ta rame cikin kwanaki biyun da basu had'u ba tasan bata jin dad'i sosai a yadda take mata bayanin irin zaman da take a gidansu................. "Baby" taji muryar prince Hamid ya kirata da sauri ta daidai nutsuwarta tana kallon sa tace "na'am Yaya Hamid kayi hakuri inata 6ata maka lokaci bada sona bane dama Ayrah zaka baiwa aron wayarka zata saka numbern yayanta Aiman ta kirashi yanzu suyi magana ta baka dan Allah" ta karasa maganar harda had'e hannuwanta shiru yai yana kallonta dahar zai tambayi ita ina tabar tata wayar sai kuma yai tunanin ko itama irin Babyn ce da Ahmad ya hanata ri'ke wayar shiyasa ya fasa fad'ar abinda yake son fad'a kawai ya fito da wayar ya mi'kawa Baby yana cewa "gashi nan idan tayi wayar ki taho min da ita ina mota" ya fad'a yana mi'ka mata kafin ya juya zuwa inda motarsa take fake numfashi me dad'i Ayrah ta sauke tana kallon Baby wacce ta mi'ka mata waya kar'ba tai cike da murna ta saka numbern nasa da yake ta ri'ke a kanta tayi sa'a kuwa tana kira ta shiga amma ba'a d'aga ba harta katse saida ta sake kira ana biyu ya d'aga tana jin ya d'aga tace. "Hello Yaya Aiman" daga can 6angaren Aiman dake zaune da littafi yana rubutu yace "na'am Ayrah yakike"? Kamar zata fashe da kuka muryarta har rawa take tace "ina lafiya Yaya Aiman ya karatu"?. "Alhamdulillahi Ayrah dama inata nemanki meyasa idan na kira wayarki Bata shiga kullum a rufe yau kuma naga kinyi kirana da ba'kuwar number me yake faruwa ne"? Hawaye ne suka fara zuba mata na kwananki da yawa da take 6oyewa yau suka fito cikin kuka tace " tun ranar da Umma tasa Daddy yaje ya taho dani ta sakashi ya 'kwace wayar wai ka bani waya badan na ri'ka kiranka bane salon na kira samarin banza ne Ina kawo gidan itace ta kar'be wayar sannan ta 6alla Sim card d'in shiyasa tun daga ranar baka sake jina ba". "Waye ya kar'be wayar a cikin su Daddy ne ko Kuma Hajiya Khubura waye". "Umma ce amma saida ta fad'awa Daddy yasa ta kar'be". "Toke meyasa daya saka ta kar'be bakije gurin Aunty Umma ta kirani kin fad'a min ba sai yau". "Daddy ne yace karna 'kara zuwa gidan yai min katanga wai yawon banza nake fita haka Umma tace masa". "Ok shikenan ki daina kukan haka yanzu zan turawa Aunty Umma dubu ashirin kije ki kar'ba ki sai wata wayar kota sha biyar ce dubu biyar d'in kuma ki barta ki ri'ka hawa napep idan zakje school ko yanxu ya baki driver da zai ri'ka kaiki ne"? Kaita girgiza tana cewa "a'a bai bani ba a kasa nake zuwa na koma" numfashi Aiman ya sauke cike da tsananin mamaki meyasa Daddy yake hakane haka kawai yadauki tsana ya d'orawa 'yar daya haifa daba haka yake ba meyasa cikin shekaru uku ya canza yana so yasan haka amma ya bari saiya dawo insha Allahu zai zurfafa bincike koda a gurin malamai ne suyi masa istahara aga abinda yake faruwa wanda su basu sani ba........... "Yaya Aiman bansan da yadda zanje na kar'bo kud'in ba saboda idan na dawo gida bana sake fita ko harabar gidan ne saidai idan school zanje". "To yanzu abinda za'ayi zan turowa Aunty Umma kud'in zan fad'a mata ta sai miki wayar inyaso idan kin fita zakije makarantar sai kibi tacan ki kar'ba kuma ki tabbata kin 6oyeta sosai kar wanda yasan kina da waya kinji"? Kaita d'aga tana cewa "to Yaya Aiman nagode sosai Allah ya saka da alkhairi Allah ya tsareka ya dawo dakai lafiya" "Amin Ayrah nima na gode da addu'a ki baiwa me wayar da kika ara yanzu zan tura mata kud'in zata sai miki". "To Yaya Aiman sai anjima". "Uhum sai anjima Ayrah" ya fad'a yana katse kiran numfashi Ayrah ta sauke tana kallon baby da murmushi akan fuskarta tace "baby nagode sosai kin taimake ni Allah ya biya ki gaskiya badan Allah yasa dake a kusa dani 'kawa tagari ba wallahi da rayuwata saita zama abar tausayawa amma koda kin ganni zan shiga damuwa kozan shiga duhu kozan kauce hanya zakiyi kokarin ki nusar dani nagode Baby" murmushi Baby tai tana girgiza kai tace "karki damu Ayrah ni dake mun zama d'aya ai babu bambanci dan kawai na amsan miki waya kinyi magana kike min godiya karki damu muna tare insha Allahu bari naje mu tafi kar lokacin sa ya 'kure" hannu Ayrah ta mi'ka mata suka gaisa kafin suka juya tare inda motar prince Hamid take saboda duk hanyar fitane daga school d'in baya cikin motar kuma a rufe take shiyasa Ayrah sukai sallama da baby ta wuce ita kuma ta jingina a jikin motar tana jiran ina ya tafi ya dawo suma subar school d'in kusan mintuna talatiin bayan tafiyar Ayrah sannan prince Hamid ya dawo kallonsa tai da alamar tambaya tace. "Yaya Abdul-Hamid ina ka tafi ne"? Shima kallon nata yai yana saka key ya bud'e motar saida suka shiga ya tada motar suka bar cikin school d'in sannan ya bata amsa "naje masallaci nayi sallah ne saboda naga baku gama abinda zakuyi ba ni kuma bana son yin sallah ni kadai nafi sonta a jam'i tafi falala" murmushi Baby tai tana kallon fuskar wayarsa tace "Yaya Abdul-Hamid na tambaye ka"? Kaiya d'aga yana cewa "tambaye ni man niba irin Ahmad bane" jin abinda yace yasa Baby tai dariya tana rufe baki tace "laaa ni bance haka ba kawai dai tambayarka zanyi meyasa ka saka photon Yaya Ahmad akan secreen d'in wayarka"?. "Oh tambayar da zaki min kenan"?. "Eh". "Saboda ra'ayi na saka sannan d'an uwana ne 'kani nane baya kusa dani yayi min nisa idan na bud'e fuskar wayata na ganshi dad'i nake ji a raina ji nake kamar na kirashi ya amsa" yana rufe baki Baby tai dariya tana cewa "to shima kenan yanzu photonka ya d'ora akan nashi fuskar wayar shima ya ri'ka ganinka kenan"? Kaiya girgiza Mata yana cewa "a'a shiba photona ya d'ora ba photon budurwarsa ne" ya fad'a yana daina kallon titi ya juyo kallon Baby yaga ya zatai zaro ido waje tai tana cewa "budurwarsa dama yana da budurwa ne"?. "Eh yana da ita". "Amma Aunty Maryam ce ko"? Da alamar tambaya prince Hamid yace "wacece Maryam kuma"? Dan shi ya manta ma da wata Maryam 'yar uwarsu. "Aunty Maryam wacce tazo kwanan baya nake fada" ko itace budurwar tasa"? Kaiya girgiza mata yana cewa "a'a ba ita bace ked'in waye ya fad'a miki Maryam budurwar Ahmad ce"?. "Ba fad'a min akai ba da idona na gani kuma kunne na yaji tace tana sonshi" zuba mata ido sosai prince Hamid yai daga baya kuma yace "ita Maryam d'ince tace tana son Ähmäd"?. "Kwarai a gaban mu ta fad'a nida Aunty Khairat tace saita aureshi wai idan ta shigo gidan mun shiga uku". "Kamar ya kun shiga uku Kuma ban gane ba"?. "Humm wai akan taga yadda yaya Ahmad yake mana shine tace da laifin da mukai da wanda bamuyi ba duk zata ri'ka fad'a masa yana dukan mu yana hukunta mu kuma mu jira dawowar ta zuwanta gidan matsayin matarsa bazai mana dad'i ba sai mun raina kanmu mune zamu ri'ka yimata wankin kayanta munayi Mata girki shara da wanke-wanke" dariya prince Hamid yai yana jinjina yace "lallai ta d'auko abinda yafi 'karfinta Ahmad take so? Tab aiko wahalar da kanta zatai a banza Ahmad bazai ta'ba sauraron taba domin shi yana da wacce yake so tunda dad'ewa itace za'bin sa ita zai aura bana tunanin yana burin zama da mace biyu daga ita ya kulle kofa". "Tofa yaya Ahmad da budurwa wai gwangwazo uhm masha Allah duk ranar dayai aure nasan shikenan matsalar mu tazama she'kak'kiya idan ya koma part d'insa ya daina zuwa gurin Momy sosai sai lokaci zuwa lokaci muma ma huta Allah yasa matar tasa ta ri'ka tsareshi a part d'insu tana hanashi fitowa ace a rana bazai fito ba saidai idan masallaci zaije ko gaida Momy" dariya prince Hamid yai harda dafe kai yana cewa "kai baby sai kace mijin tace zata tsareshi a gida Ahmad d'in ne zai yarda ayi masa haka kamar kin manta waye shi"?. "Ai kuma Yaya Hamid ba anan take ba sai kaga duk wannan zafin nasa yazo yai sanyi idan yai auren kai kuma da baka da zafin sai kaga ka zama kaine me zafin hakan na iya faruwa". "Ke yanxu a tunanin ki akwai macen dazatasa Ahmad yai sanyi"? Cikin 'kwarin gwiwa Baby tace "sosai ma wuya yai auren irinsu Yaya Ahmad su mata ke juyawa kamar waina wallahi kuma zakace nina fada maka muna nan sai kaga yadda ya Ahmad zai koma musamman idan matar tasa ta iya soyayya ta iya kisisina da karairaya humm ya Ahmad yana son soyayya ai na gama karantarsa" dariya ce sosai ta kama prince Hamid ya kalli Baby yana cewa. "Ashe dama haka kika sakawa Ahmad ido bai sani ba taya kikasan yana son soyayya"? Prince Hamid yai mata wannan tambayar yana 'kureta da kallo saboda duk zatonsa ko su Momy sun fad'a mata Ahmad nasonta to amma dasun fad'a mata bazatace dama Ahmad nada budurwa ba kawai kintace tai ta fad'a......... "Nifa ban saka masa ido ba kawai yanayin sa na gani nace zaiso soyayya ba sani nayi ba abar maganar ma haka kar naje nayi 6arin zance" ta fad'a harda kama bakinta murmushi yai yana mayar da hankalinsa kan titi daidai sun isa kofar gate d'in aka bud'e masa ya shiga direct saida ya kaita har kofar part din Momy ta sauka sannan ya wuce zaikai motar gurin aje motocin masarautar. Babu kowa a parlor dan haka Baby bata tsaya ba ta shige part d'insu a kwance ta samu Khairat rungume da pillow ta kashe murya suna waya da Shadad tsaye tai tana kallon ta daga baya kuma tai dariya tana karasowa ta kalleta tana cewa "kaga masoyan zamani irin wannan kashe murya haka tabd'i wannan gaba zamusha kallo idan kukai aure saidai mu ri'ka rufe idonmu saboda karku makanta mu kusa mu koma yawo da sanda" ta fad'a tana kallon yadda Khairat d'in take murmushi tana sake gyara kwanciya batasan ma me Babyn take fad'a ba hankalinta yana kan wayar da suke ha6a baby ta ri'ke cike da mamaki tai dariya tana aje handbag d'inta tace "to wannan gara na bari ki gama tunda ba jina kike ba kafin nan tsaya nayi alwala nai sallah" toilet ta wuce tayo alwala tazo tai sallah harta idar tai addu'a ta tashi Khairat bata gama ba murmushi Baby tai tana kallon ta ganin itama Khairat d'in ita take kallo yasa ta girgiza mata tana nuna mata da hannu cewa ta tafi dinning taci abinci d'aga mata kai Khairat tai yayin da Baby ta fita tana sake dariyar da batai niyya ba wato saboda kartai magana su katse hirar da suke shine take mata maganar kurame da hannu da ido fita tai tana zama a dinning hankalinta kwance saboda tasan ko kwana zatai a gurin Ahmad baya nan balle taji fargabar karya shigo ya sameta ita kad'ai. *Da dare bayan Daddy ya dawo gida yake fad'awa Hajiya Khubura cewa Aiman ya kirashi yana tambayar meyasa suka kar'be mata waya zai sai mata wata amma wallahi suka qara karbewa zasuga tashin hankali irin wanda basu ta'ba gani ba jin sa'kon da Aiman ya bayar a fad'a mata yasa ta kalli Daddy a she'ke tana cewa. "Au nan d'in kiranka yai yake tuhumarka mun kar'be waya a gurin Ayrah saboda ya gaji sharri da rashin kunya to an kar'be d'in kuma baza'a bayar ba idan ya sake kiranka ka fad'a masa haka in jini d'an mara mutuncin yaro kawai". "Nidai duk ba wannan ba bana son tashin hankali a gidan nan idan ya sayo mata wata karki sake karbewa ke kyale mata kayarta bana son yawan hayaniya". "Me kake nufi na kyale ya ri'ka cimin mutunci kenan ina kallonsa kome"?. "Ni bance yaci miki mutunci ba saboda ke uwace gareshi kawai dai nace ki daina shiga safgar wannan yarinyar yana kirana yana damuna da maganar ta bana so kin gane"? Shiru Hajiya Khubura tai cike da takaici hum wato nan Aiman 'kararta yakai gurin Daddy akan ta kar'be waya aiko wallahi ko yanzu ya sake sayowa Ayrah wata saita kar'be ta idan yana ganin bazata iya ba yasayo matan ya gani ko yana gari zatai fin hana balle baya nan har ji tayi ta matsu gari ya waye ta jawa Ayrah kunne tayi mata tas akan wannan maganar. Washe gari tun asuba Ayrah tana gama had'a musu breakfast tabar gidan zatai school suka had'u da 'kanwar Aiman ta bata wayar daya turo kud'i a sai mata sannan ta bata dubu biyar d'in a take kuwa tahau napep sannan ta kirashi tayi masa godiya sosai a ranar ta wuni cikin walwala da jin dad'i wanda ko Baby saida taji dad'in yadda taga Ayran ta samu farin ciki shiyasa ta bata shawarar cewa duk yadda zatai karta bari su Hajiya Khubura suga wayar ta ri'ka 6oyeta. Kamar yadda Boukar ya kira mahaifiyar Sabit ya fad'a mata sati biyu tsakani su Niseh suka kammala exam ta tattaro suka sauka da yake saukar dare sukai gidan da Boukar ya kama anan suka kwana amma tun daren sukaje ya nuna mata gidan sannan suka dawo washe gari da wuri suka tashi sukai shirin zuwa amma banda Boukar yana gida sakamakon shi abokin Sabit ne bai kamata ace Sabit ya ganshi a gurin ba duk da mahaifiyar sace ta sakashi amma abun babu dad'i sannan shi kansa Boukar din baya goyon bayan auren da Sabit yayi yafi son ya auri bayerabiya irinsu. Nadiya tana zaune a parlor ita kad'ai sai me aikinta da take ta faman yi mata hidima daga wancan tai wancan amma duk da haka bata gwaninta sai tsawa da bala'i da zagi Nadiya take aika mata wani lokacin harda dukanta take idan tai kuskure wajen yin wani aikin yanzun ma tana zaune bayan ta gama yanka Mata kayan marmari tasa ta kunna mata TV tazo kuma ta bata 'kafofi tai mata tausa suna cikin haka sai gani sukai an bud'o kofa an shigo mace fara tar 'katuwa tana juyi da mamaki Nadiya take kallonta yayin da Seemah ta mi'ke jiki na rawa tace "barka da zuwa Hajiya bismilllah sannu karaso" (ba shishshigi taiba Nadiyan ce ta umarceta cewa idan tayi ba'ko ta ri'ka tararsa a madadinta saboda ita bakinta bazai iya wannan wahalar sannu da zuwan ba🤔) wani irin kallo Nadiya take binta dashi ganin kamar ba bahaushiya bace ga kuma yadda take 'karewa gidan kallo jin Seemah ta sake cewa. "Karaso Hajiya shigo ciki" yasa Nadiya sakar mata harara zatai magana Seeman tace "ranki ya dad'e a kawo mata abun sha wanne kala" yatsina fuska Nadiya tai cikin wula'kanci da nuna 'kyama tad'an toshe hanci tana cewa "what wannan halittar zance ki kawowa abun sha a gidana nasan daga bolar da take yare cefa? Zaki 6ace min da gani ko saina d'auke ki da mari"? Ta fad'a cikin tsawa da gudu Seemah tabar gurin tana wucewa ta koma kitchen inda ta fito qarewa matar kallo Nadiya tai cike da mamakin me yakawota gidanta tace. "Madam wanne irin abune wannan zaki shigowa mutane gida sakaka haka kara zube ko an fad'a miki nan gidan arna ne ba sallama wacece ke daga ina kike zo me kike nema? Wani irin ba'kin kallo matar taiwa Nadiya batare data bata amsa ba ta zauna akan kujera tana d'aga waya ta kira "hello Niseh ina Naomi din ku shigo me kukeyi a waje ku karaso man gidan nefa wallahi sai naci uban Sabit tunda ya nuna ban Isa dashi ba ashe da gaske ne abinda ake fada akansa naga yarinyar a yanzu haka tana gabana tana kallona". Jin abinda matar tace yasa gaban Nadiya ya fad'i a ranta tace innalillahi wa inna ilaihi raji'un na shiga uku wannan ita kuma wacece a familyn su Sabit me yai mata take zaginsa da 'kwarin gwiwarta kamar wata mahaifiyarsa................ Shigowar 'yan mata biyu yasa suka katse mata tunanin da take hankalinta ta mayar kansu kamar su d'aya tsayinsu daya komai nasu iri d'aya da alama 'yan biyu ne abinda yai mugun d'aga mata d'aga hankali shine ganin yadda suke kama sosai da Sabit d'inta har dogon hancinsa da yanayin tsayawar gashin girarsa sake kallon matar tai taga itama dai kamar suke da Sabit d'in to su waye wadannan daga ina su kuma tasan dai wannan matar ba mahaifiyar Sabit bace tunda tasan tasa uwar tana rijiyar zaki to ita kuma wannan wace ita mene ala'kar su ko kanwar mahaifiyar sace da yaranta....................... Cikin tsawa taji matar tace "ke bahausiya ina Sabit meyasa zaki aureshi kinsan yadda na tsani hausa wayasa ki aureshi"? Jin abinda take yasa a dake cike da jin haushi Nadiya tace "na aureshi d'in ki Hana tunda kece kika haifeshi tukuna ma tsaya wace ke zaki zo min gidan mijina ki tada min hankali kiyi gaggawar barin nan kafin na kira miki hukuma dan wallahi bakisan wace niba gani na kawai kikai yanzu bani da mutunci nafi bala'i zama fitina kin gane dan haka ki kama kanki". Tunda ta fara magana matar take kallonta jin abinda tace yasa matar cire mayafin dake kanta ta d'aure shi a 'kugu tana cewa "yau zan nuna miki karshe masifar da bala'i kin tari abinda yafi karfinki yarinya daga yau zaki kiyaye tarar mace irina dama nasan bazakiyi tarbiyya ba daga ganinki rainon mace ce ke" hannu Nadiya ta d'aga mata cikin taratsi tace "karki kuskura ki zagar min mahaifiyata naji kina wani ni rainon mace ce ki fad'a min wanda namiji ya raina look madam kubar nan ku fice min daga gida kafin nai muku hauka zan gwada muku tashin hankali da d'anyan kai". Kai madam ta jinjina tana cewa "bari mu fara gwada miki namu aike da bakine kike maganan mu kuma da dantse zamu gaya miki Niseh a shirye kuke"? Jin abinda suka ce yasa Nadiya ta fahimci Shirin nad'a mata duka suke da sauri ta d'aga waya jikinta har mazari yake tana kiran Sabit amma bai d'aga ba kusan kira hud'u wayar Sabit bata hannunsa tana bedroom ya barta jin bai daga ba yasa ta ta kira Abidah ko sallama babu tana d'agawa a hargitse Nadiya tace "hello Abidah kina jina kizo gidan nan yanzun nan" jin abinda tace yasa Abidah cewa "nazo kuma Nadiya meya faru zanzo gidanki ina school fa" "Eh ki baro school d'in kizo yanzu ina jiranki a parlor karki tsaya sanya ki taimaka". "A'a gaskiya indai zanzo ma saidai idan an tashi daga school wajen karfe biyu da rabi" zaro ido waje Nadiya Tai tana kallon yadda su Niseh suke harararta suna hura hanci tace "kinyi hauka ne kinsan masifar data sameni zakice wata uwa saikin tashi daga school zaki zo sannan idan farfesu nane ma anyi an shanye romon ko"?. "Ban gane ba Nadiya wai meya sameki ne kuma bayan naji muryarki normal baki da lafiya ne ko kuma wata matakalar ce dabam"?. "A'a lafiya lau kawai wasu karfofi ne suka zo min gidan harsu uku uwa da 'ya'yanta sai ba'ka'ken maganganu suke fad'a min dan Allah kizo yanzu akwai bala'i domin bansan daga inda wadannan masu siffar aljanun suka zo min ba". "Ok gani nan ina zuwa gara na ha'kura da lesson d'in na taho kar suyi miki illa bari nazo muci uwar shegu mu kwana lafiya" tana fad'in haka ta kashe kai Nadiya ta jinjina tana kallonsu tace "humn 'karyar ku ta 'kare yau ku jira zuwan sister na wallahi saimun 'bab'balla ku yadda kuke d'in ba dan kun ganku d'irka-d'irka girman banza ne ba tsoron had'a damtse daku zamuji ba" Nadiya na rufe baki Sabit ya shigo kamar an jefoshi dawowar sa kenan daga anguwa ganin wacce ke zaune a parlor yasa lokaci guda yaji numfashinsa na neman ficewa daga jikinsa hankali tashe ya karasa gumi na tsastsafo masa na tsantsan tashin hankali da rashin gaskiya yace "Mah kece ko ido nane yake ganin kamar ked'in ce dama kinsan gidan da nake ne sannu da zuwa" hakan ma da'kyar ya iya fad'a tsabar watsattsan kallon da yaga tana yi masa jiki a sanyaye ya karaso yana dur'kusawa a gabanta ya sunkuyar dakai domin baisan me zaiyi kota Ina zai fara ba yasan wace mahaifiyarsa mace ce mafad'aciya ganin yadda Sabit yai da kuma sunan daya kira matar yasa Nadiya ta bud'e baki tana shirin magana ba zato taga matar ta d'auke fuskar Sabit da maruka a wanda a firgice Nadiya ta ri'ke nata kuncin kamar ita aka mara idonta kuwa kamar zai fito waje ya fad'o kasa tsabar yadda ta zaro shi batare da tasan tayi hakan ba sai matar da take kallo a firgice lokaci guda tsoro ya rufeta.............. Da yatsa Mah ta nunata tana cewa "ke yar matsiyata na dawo kanki uban wa yasa ki aure min d'a kinsan yadda na tsani had'a jini da wanda ba yarena ba dama dana hana Sabit ya aurenki shine daya gama school ya dawo ya aureki yai min karyar yana Cotonou hummm yau kuwa zan nuna miki kuskuren auren da uwar miji bataso akayi saina gwada miki rashin imani a gidan nan wato Sabit harda uwar 'karya ka siya anan itace ta shige maka gaba akai auren matsayina humm ka za'bi wata tai maka uwa ta maye gurbina saboda ni bana so yanxu fad'a min a ina matar take naje naci ubanta na had'ata da hukuma su hukunta min ita irinsu ne masu bata al-umma ka sayeta da kudi tayi maka aure da yake tsinanniya ce ke kuma yanxu zakici ubanki Sabit saiya sakeki". Tunda ta fara magana jikin Nadiya yake rawa da kakkarwar tsoro jin karshen maganar ta yasa ta d'ora hannu aka tana fashewa da kuka yanxu kam idan ta fahimta duk abinda ake wannan itace asalin mahaifiyar Sabit sunzo ne daga Lagos batasan yayi aure ba matar daya d'auka anan kud'i ya bata taje musu matsayin itace mahaifiyar sa ta shiga uku da tasan Sabit bashi da mahaifa a kusa wallahi bazata ta'ba auren saba yace mata daga Lagos d'in suka dawo nan Kuma itama wancan matar karyar datai Mata kenan tace sun dawo nan da kasuwanci ne kuka take sosai tana yarfa hannu saboda tasan yanxu ta shiga tarko da sauri ta dur'kusa a inda take tana cewa. "Dan Allah kiyi hakuri madam wallahi bansan cewa matar daya ara anan ba mahaifiyar sabace wata mata ya nuna min itace ta wuce masa gaba akai komai ni bai fad'a min shi d'an Lagos bane yace min sun dawo nan da zama shida mahaifiyar sa ne shiyasa ma na aureshi" kamar Mah batasan komai ba ta kalli Sabit wanda ya sunkuyar dakai tana cewa "au Sabit harda uwar karya ka saya saboda kana son ka auri hausa"? ta tambaye shi tana d'aga hannunwanta duka biyun sama ta d'amesu ta zuba masa duka a baya ganin yadda Mah take dukan Sabit yasa Nadiya ta sake susucewa to d'anta ma take masa irin wannan dukan inaga ita kuma watakil kasheta zasuyi............. Bata gama tunani ba taji Mah tace "me kuka tsaya kallo ina dukan Sabit kun zuba min ido ku daka min ita yau sai jikinsu yayi tsami sannan ya saketa dan ubanta "Mah tana rufe baki su Niseh suka rufu akan Nadiya suka fara sambad'arta Abidah shigowar ta kenan ganin yadda suke dukan Nadiyan yasa da gudu ta karaso tana fincike Naomi tace "mitsiyata kashe min 'yar uwa zakuyi ubanku ne ya jawoku gidan tsinannu asararrun karnuka" Abidah ta fad'a itama tana rufe Naomi dake tsaye da duka ganin haka yasa Mah ta taso ta shiga cikinsu Niseh suka hau musu du'ka su uku tuni suka fara ihun neman taimako Nadiya sai kiran Sabit yazo ya taimake ta take yana zaune yana kallo baida ikon koda magana ne balle ya ceceta saida sukai musu duka son ransu musamman Nadiya sunfi dukanta akan Abidah d'agowa mah tayi tana huci ta kalli Sabit tana cewa "Kai Kuma zaka saketa ne ko saina dawo kanka"? Kaiya girgiza da sauri ya kalli Nadiya wacce ke kwance a kasa tana kuka yace. "Dan Allah Nadiya kiyi hakuri 6oye miki ainishin mahaifana danayi ba ina nufin yaudararki kona cutar dake bane son da nake miki neya jawo haka bansan waye ya fad'awa mah tazo nan ta sameni ba dan Allah ki yafe min wallahi ina sonki amma babu yadda zanyi mah bazata barmu mu zauna ba............ "Dan ubanka Sabit bayani nace ka zauna kayi mata ai tasan ba yaudararta kayi ba tunda ka aureta nace ka saketa ko saina karasa kasheta daka gane" ta fad'a tana take 'kafar Nadiya 'karar azaba ta saki wanda Sabit kuma ya saki ihu ganin tana neman karyawa Nadiyan 'kafa yace "please Mah dan Allah........... "Sabit zanci ubaka fa ka rufe min baki nace ka saketa kai nake jira zamu tafi"? Kaiya girgiza wanda ganin abinda yai yasa Mah ta kawo masa mummunan duka da sauri ya matsa baya cikin tsawa tace "Sabit Sabit kasan ni fa kasanni fa ka guji fushina walay zan kashe kafa kasanni ka saketa nace" jikin Sabit yana rawa ya kalli Nadiya wacce ke girgiza masa kai alamar karya ce ya saketa shima kan ya girgiza mata yana cewa. "Kiyi ha'kuri Nadiya na sake ki" yana fad'in haka Nadiya ta fasa 'kara tana d'ora hannu aka ta kuma fashewa da sabon kuka mah dake tsaye harara ta sakar mata tana cewa "ban gamsu ba Sabit ba saki d'aya nake soba saki uku zakai mata bazaka sake dawowa arewaci ba har abada muna komawa zaka tafi London kaci gaba da karatu acan idan ka dawo saika nemi yarenka ka aura kayi mata saki uku inaji babu maganar aure tsakanin ku agaba" babu yadda Sabit ya iya haka yai mata saki uku mah ta saka ya d'auko takarda da biro ya rubuta mata duk abinda yasan kayansa ne a gidan ya tattare tas ta sakashi gaba yana kallon Nadiya yana zubar da hawaye itama haka tana mi'ka masa hannu ta kasa tashi baida damar daya isa dosar inda takema balle ya ta'ba ta suka fice daga gidan ihu Nadiya taita kurmawa kamar muryarta zai fashe Abidah data mi'ke da'kyar gefen fuskarta harya fara kumbura da bakinta da'kyar taja 'kafa taje inda Nadiyan take ta d'agota tana cewa "amma dai Allah ya tsinewa wannan matar Allah yasa baza suje gida lafiya ba kiga yadda ta fasa miki goshi"? Nadiya dai batai magana ba sai kuka da take a hakan kowa tana jan'kafa suka fita waje motar Abidah tana can wajen gate d'in saboda bada ita ta shigo ba me gadi yana zaune yana kallonsu suka fita kaiya girgiza yana sakin murmushi domin jiyan nan ta fito ta tsiyata shi saboda Seemah ta kawo masa abincin Sabit bata sani ba zagi harda na 'kyama ashe itama washe gari daula zata 'kare a koma gidan innah. Ba gida suka wuce daga Nan ba saida suka bi ta chemist akaiwa Nadiya bandage ita kuma Abidah aka bata magani saidai yadda Nadiya take jin ciwo a cikin 'kafarta tasan da matsala amma ta bari suje gida tukuna sai a kira mata likita har gida saboda wani irin zazzafan zazza'bi ne ya rufeta humm tashin hankali wanda ba'a saka masa rana Hajiya Khubura har tafisu ihu da kuka lokacin data gansu da kuma bayanin da Abidah tai mata ga takardar saki reras har uku sannan ta kad'a Sabit sun tafi yankinsu ga zazza'bi da kuka Nadiya ta dameta lokaci guda taji hawan jininta yana neman tashi da'kyar ta lalla6a bedroom d'inta tasha magani sannan ta samu damar kiran likita yazo har gida ya duba Abidah da Nadiyan saidai yace Nadiya ta samu targad'e a 'kafarta da kuma gocewar 'kashi dole saidai a kaita asibiti a gyara mata gara Abidan ita iya kumburi ne Nadiyan sukafi duka saboda gurinta suka zo, a take sukai asibiti da Nadiya akai mata gyaran dole Hajiya Khubura ta zauna acan Abidah kuma ta dawo gida tai musu abinci ta koma............... HUMM MUJE ZUWA ✍️MRS ÄL'ÄMËËÑ ÄHMÄD ÇË. WhatsApp no:+234 816 098 3083 yusrahmusaabubakar@gmail.com TYPING📲Sun, Ap/6st/25 10:00am ✍️Yusrah Musa Abubakar Gimbah 👑 ROYALTY 👑 In the name of Allah the must benefits and the must merciful ALLAH THE MOST HIGH DOESN'T SLEEP ALLAH THE MOST HIGH IS PURE HE ACCEPT ONLY WHAT IS PURE. Manzon Allah SAW May the blessings and the peace of Allah be upon you ya rasulullah muna sonka fiye darai da iyaye da dukiya you have no limits ya Annabi💓. 💔ZUCIYAR ALIYU CE💔 NEXT BOOK D'INA KENAN ZUCIYAR ALIYU CE ITAFA YARINYAR ZUCIYAR ALIYU CE ME KUKE TUNANI FANS KU KASANCE TARE DANI AKWAI AIKI A GABA INSHA ALLAHU ZUCIYAR ALIYU CE ZAI FARA SAUKA MUKU DA IZININ ALLAH DANA KAMMALA WANNAN. Masu bu'katar littafai na kofa a bud'e take akwai free akwai paid duka wanda mutum yake bu'kata zai samu amma fa bana tura free sai an sayi paid book d'ina ehe karma mutum yace na tura masa alakoro😂. Free book. Yarima abdul-maleek D'an millionaire Husnah ko Badiyat Me kamar sarki book 1 Minister Ashraf book 1 Safreeyyah book 2 Paid book Me kamar sarki book 2 #300 Minister Ashraf book 2 #300 Safreeyyah book 2 #400 Ga duk mai bu'kata zaka iya yi min magana ta WhatsApp number na +234 816 098 3083 Yusrah Musa Abubakar ina maraba da kowa. Nifa I have no girman kai if you fushi dani to wallh you are just 6atawa kan/ki lokaci 🤣 haka nake bani da haushin kowa kuma kowa nawa ne. Bismilllahir Rahmanur Rahim 📿 16~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Nadiminah @YUSRAHMS CE Page 31 & 32 Abun duniya ya damu Mama ganin idan Maryam tai kiran Ahmad a waya baya d'agawa tunda ya tafi bata ta'ba kiransa ya d'aga ba wani lokacin ma idan ta dameshi da kira kashe wayar yake ko yasata a silent sannan ta WhatsApp ma idan tai masa magana bazaiyi mata reply ba harya sauka takaici ne ya ishi Mama ganin yadda Maryam ta shiga damuwar rashin kulawar da Ahmad yake nuna mata dan haka taje har gida ta karantawa wata 'kawarta Hajiya Habiba ga abinda yake faruwa dan Allah ko tasan yadda za'ai hankalin Ahmad ya karkato kan Maryam yaji duk duniya duk cikin yan mata babu wacce tai masa sai ita a take Hajiya Habiba tace tabbas da akwai wacce zatai mata wannan aikin da zarar tayi baza'ai sati ba sai hankalinsa ya dawo kanta bazai samu nutsuwa ba sai yaji muryarta tasha kai mutane ana yi musu magani kuma suna dacewa jin wannan bayani ya faranta ran Mama ta take ta kira Maryam tana school tace ta baro makarantar tazo zasu je anguwa tana gidan 'kawarta tazo nan ta sameta, suna zaune Maryam ta shigo jikin Mama har rawa yake suka fita ta ciri kud'i suka tafi gidan Hajiya me bada maganin farin jini. Layi kuwa suka samu sosai kamar wanda sukaje ganin likita haka mata ke tururuwa a gidan kuma zamansu ma sama da mutum goma sun sake shigowa kusan wuni sukai kafin su samu layi yazo kansu suka shiga d'akin da matar take tana zaune a cikin magunguna kanta ko d'an kwali babu tayi wani irin hargitsastsan kitso ta zane fuskarta da ba'ki sai zare ido take yi zama sukai Mama dai sai kallon ikon Allah take ganin yadda Hajiya Habiba ta ware suke zance harda dariya kodan ba abun mamaki bane tunda tace sun saba anan take kar'bawa yaranta magani kafin suyi aure da bayan sunyi auren bayanin abinda ke tafe dasu Habiba tai mata sannan ta fad'a mata maganin farin jini suke bu'kata, kallon Maryam me maganin tai tana jinjina kai tace. "Kina sonshi sosai ba? Kuma kina so ki aureshi haka ne"? Tun kafin Maryam tai magana Mama data fita za'kewa tace "haka ne wallahi daidai ne abinda kika fad'a gaskiya ne" hannu ta d'aga tana cewa "ba dake nake ba wacce aka zo dan ita nake tambaya" shiru Mama tai tana kallon Maryam da ta'ki magana da ido ta nuna mata ta bata amsa murmushi Maryam tai tana cewa "eh haka ne abinda kika fad'a akansa gaskiya ne amma shi kwata-kwata hankalinsa baya kaina bai damu dani ba ko kiransa nayi a waya baya d'agawa idan yaga zan takura masa da kiran ma saiya karshe wayarsa wannan shine damuwa ta indai da yadda za'ai ya soni ya kaunace ni fiye da yadda yake son kansa ya susuce a kaina ya manta inda yake ya daina samun nutsuwa da zaman lafiya idan bai ganni ba ko yaji muryata" Maryam na rufe baki Mama tace. "Farko fara a Bata maganin farin jini idan har tana da farin jini duk wannan abun bazai samu ba tayi masa kwarjini kawai dan Allah a taimaka a bamu a fad'i abun sadaka nawa ne"? Mama ta fad'a tana kokarin zuge zip d'in jakarta. "Bana yankewa ko nawa ne kawai aje min ake ko naira biyar ce itace karamin kud'i" cewar me magani tana 'kure Maryam da kallo kamar me tunanin wani abu kaita jinjina tana d'agowa ta kalli Mama sai kuma tai murmushi tana sake mayar da hankalinta kan Maryam tace "amma fa wannan sai kunyi da gaske domin gaskiya yana da zazzafar zuciya sannan ko kad'an bata gabansa bata ransa babu ruwansa da ita har gobe haka abun amma tunda kunzo nan kusa a ranku ta faru ta 'kare bashi daja indai na fara yi muku aiki a kansa aure kam saiya aureta dolensa". Kai Hajiya Habiba ta jinjina dakyau cikin yardar da taiwa matar tace "kwarai wannan maganar taki haka take a zaune gaskiya ne ko bayaso dole ya amsa Kira indai kika kirashi" mayar da hankalinta kan Mama tai tana cewa "kawata karki damu kinzo gurin da za'a kar'be ki hannu biyu kuma a share miki hawayen ki dan haka karki tsaya sanya ki bata abin sadaka yadda kika ji ranki yaga damar bayarwar ita ba yanke kud'i take ba amma ki sani tana yanke damuwar mutum indai anzo gurinta" jin abinda Hajiya Habiba tace yasa Mama bud'e jakar ta saka hannun ta dam'ko kud'i dubu hamsin ta aje tana cewa "biyan bu'kata yafi dogon buri indai zatai farin jini tai kwarjini bani da matsala ko nawa ne zan kashe daga kan dubu d'aya zuwa million d'ari na tabbata idan na samu ya aureta kud'in dana 6atar zasu dawo saboda ina fad'a miki ranki ya dad'e me magani yaron da nake so ta aura millionaire ne gashi Kuma jinin sarauta kyau da diri iya d'aukar wanka gashi soja 'kak'karfan gaske jarumi ma kuwa idan na tsaya kwatanta miki shi zamu iya kwana anan ban gama ba saidai na ta'kaita ta ko'ina Ähmäd yayi wallahi burina kawai naga mun samo kanshi". Kai me magani ta jinjina tana cewa "karki damu Hajiya indai batun farin jini ne anzo daidai wajen 'yarki ta samu kisa a ranki kamar ta auri wannan saurayin wanda kike so ta aura ne wuya ta fara indai tabi yadda nace mata bisa 'ka'ida zata dace". Cikin tsananin farin ciki Mama tai murmushi tana sau'ke daddad'an numfashi tace "yauwa nagode sosai idan zamu dawo mene abun sadakar sannan ya ake aikin"?. "Zan fad'a muku abun sadakar da zaku zo dashi a gaba amma ba yanzu ba sai shi saurayin ya dawo da zarar kun samu labarin dawowarsa kar kuyi 'kasa a gwiwa ku dawo gareni zan karasa baku babban sirrin da zaku ri'ka yi wannan ta ri'ka wanka dashi yanxu kafin ya dawo wannan kuma ta ri'ka turare yana bin jikinta a hankali ya zagayeta kafin ya dawo ta tsumu sannan idan ya dawo zan bata sirrin wanda zata ri'ka kwalliya dashi indai har shi wannan saurayin ya d'aga ido ya kalleta wallahi tallahi kunji na rantse ko? Saiya susuce ya manta inda kansa yake akanta ya sota fiye da yadda yake son kansa kuma bazai barta ba saiya aureta me kankat kenan". Jin wannan daddad'an bayani yasa Mama shiga yanayi har tana sauke numfashi me sanyin gaske a hankali ta dafe saitin zuciyarta tana murmushi kafin ta kalli Maryam tana jinjina kai tace "masha Allah haka nake son ji na tabbata yanzu kam dole Ahmad ya shiga tarkon mu ko baya so sannan itama Aunty Hauwan ko itace bata so indai Ahmad d'in ya gani yana so babu yadda zatai dashi dole ta barshi ya aureki" mayar da hankalinta kan me maganin tai tana cewa "yanzu dame zamu dawo idan har shi Ahmad d'in ya dawo"?. "Idan zaku dawo ku taho min da powder wacce take shafawa a fuska da kwalli wanda zata ri'ka sakawa a cikin idonta dasu zanyi muku maganin daya kalleta zaiga fuskarta tana fitar da haske da annuri powder zata kara mata kyau a idonsa sannan daya ya had'a ido da ita wannan 'kwallin data saka zaiji duk duniya babu wanda yake so yake son aura sai ita sannan zan bata sar'ka wacce zata d'aura wuyanta ita kuma amfaninta idan har ya kalli wannan sar'kar shikenan ta mallakeshi tas ta gama samun kansa ta samu zuciyarshi idan hakan ya faru daga wannan lokacin shikenan labari zai sauya salo zakuga abun mamaki daga gareshi abinda zaiyi akanta baza'a ta'ba tunanin ba zai haukace ne a kanta ya zama mara nutsuwa bayan duk awa biyu zuwa uku idan bai ganta ba kunsan mene hikimar? Da sauri suka girgiza kai a tare Mama harda gyara zama tana sake matsowa kuda me maganin taji yaya meye hikimar cigaba da musu bayani tayi "idan ya kasance baya jin sassauci idan bai ganta ba rashin nutsuwar sa da susucewarsa zaisa mahaifansa su sakashi ya aureta kobai shirya ba kuma koda ace bashi da niyyar hakan a ransa zamu sanya masa dole yabimu yayi abinda muke so zaku iya tafiya kuje da wannan d'in tana wanka da turare kafin dawowarsa saina ganku ku kula sosai a aikin banda mantuwar sharud'a ko sa6a lamba kunji"? mi'kewa sukai Mama na cewa. "To ranki ya dad'e mun gode sosai da taimakonki garemu sai kin ganmu" kaita d'aga bata sake magana ba har suka fita daga gidan motar da suka zo da ita tana waje a inda suka barta fuskar kowaccen su da farin ciki suka shiga mota suka d'au hanya kasa nutsuwa Mama tai saboda wannan nasara da suka samu hai take suje gida Maryam ta fara wankan maganin daga yau d'in nan ita kad'ai sai murmushi take yi zuwa wani lokaci ta kalli Hajiya Habiba tana cewa "kai amma fa alhamdulillah na godewa Allah Hajiya Habiba dama haka kika san gurin masu magani ni harna tsaya wahalar da kaina a banxa ga inda zaka zo ka biya kud'i bu'katar ka ta biya lokaci guda kaima"? Ta fad'a cikin mamaki tana kallon Hajiya Habiba wacce tai murmushin itama tana cewa. "Humm ai wannan kad'an daga aikinta nake fad'a miki ko matsayin da nake Kai yanxu da taimakonta ne sannan kishiya da Alhaji yaso yayi min nan ma ina fad'a mata ta da'kilar da maganar har gobe bai sake tasa zancen aure ba kusan shekara takwas ke bari na ta'kaice miki zance a yanzu haka wasu miliyoyin kud'i nake bu'kata daga wajensa da wajen abokan aikina amma ganin nayi bi bazam samu ba na fad'a mata da sanar matan kwana biyu jiya sun turo min kud'in shi kuma Alhaji yace idan ya fita office zaiyi min transfern nasa ne bai shigo ba maybe network ko ya manta bai turo min ba shiyasa kina karanta min matsalarki naji ya kamata kema na kawo ki gurinta ta taimaka miki naji dad'i shine gari domin nikam tayi min ba sau daya ba kuma naga sakamako me kyau kema ina tabbatar miki daya dawo ta karasa kammala abinda tace ku kawo mata shikenan an wuce gun wallahi 'yarki saita aureshi saita zama matarsa gimbiya saita auri d'an sarauta kamar yadda kike buri. D'aga hannu sama Mama tai da sauri tana cewa "Allah yasa Habiba Allah ya tabbatar mana da wannan rana nagode nagode sosai tsaya anan na fita ni gida zan wuce Maryam kuma ta shiga gidan naki ta d'auko motarta ta koma school saikin jini" Mama ta fad'a tana bud'e murfin motar ta fita. "Ok nima nagode sai anjima ki gaida gida Halima" Hajiya Habiba tai maganar tana yiwa me gadi horn ya bud'e mata gate suka shiga Maryam ma godiyar sosai tai mata sannan ta dau'ki motarta ta fito a waje ta samu Mama dan haka ta tsaya ta d'auketa takaita har gida sannan ta koma school a ranar duk su biyun wuni sukai da murmushi akan fuskokinsu ganin Ahmad ya shigo tarkon su........... 🤣TAB WALLH KUNA KWALE-KWALE AHMAD SAI BABY BAZAMU YARDA DA WANNAN BA FANS KU KWANTAR DA HANKALIN KU AHMAD YAFI KARFIN SU BABU YADDA ZASUYI DASHI YA ZAMA 'KASHIN CIKIN TURMI MAGANIN WADAN KARE😁. **Ganin yadda 'kafar Nadiya ta kumbura duk da an gyara mata ga kwanaki sunja amma babu sauki yasa Hajiya Khubura ta cika da fushi tai dam Daddy daya tashi daga gurin aiki yaje gida ya d'auka za'a sallamo su akan lokaci amma sai khaleel yake fad'a masa yauma likita yace baza'ai mata sallama ba saboda kafar batai sau'ki ba gocewar'kashi nata bai daidaita ba shiyasa Daddyn yace khaleel ya tu'ka shi a mota ya kaishi ya sake ganota tare suka je asibitin mamaki ne ya kamashi ganin irin dukan da Nadiyan tasha duk tabo a jikinta domin ranar da abun ya faru da dare yazo dubata baisan haka jikinta yake ba sai yau bayan ya dubata sun fito ya samu Hajiya Khubura a inda suke zaune karasawa yai yana cewa "subahanallahi wadanne irin mutane ne sukaiwa Nadiya irin wannan dukan kamar su goma duk sun kumbura mata jiki gashi har yau bata jin dad'in jikin nata a garin yaya ina mijin nata" kamar Hajiya Khubura zata fasa kukan ba'kin ciki tace "wanne mijinta? bayan mitsiyaci yana gurin uwarsa tai mata dukan tare da 'kannansa su biyu Ashe tsinanne mutanen da suke kawo kayan aurensa duk ba 'yan uwansa bane itama munafikar matar data zo matsayin uwarsa ashe uwar 'karya ce siyanta yayi da kud'i asalin mahaifiyar sa tana Lagos karatu kawai yake anan kuma ya gama yayi Mata karyar bai gama ba ya dawo ya auri Nadiya aka samu wani d'an ala tsinan ya kirata awaya ya fad'a mata shine suka zo tasaka yai mata saki uku sannan sukai mata duka harda Abidah da taje gidan" kai Daddy ya girgiza yana cewa . "Allah ya rufa asiri Allah ya tsare gaba kin ga irinta ko dama abinda nake fad'a miki akan a tsaya ayi bincike kikace a'a ga ranar nadama tazo tun ba'a je ko'ina ba shikenan ai nizan tafi gida Allah ya sauwake" yana rufe baki tace "ai basu ci banza ba zan nuna musu tana da gata saina d'aukar mata fansa jira nake Allah ya bata lafiya" jin abinda tace yasa Daddy yace. "A'a karki soma cewa zaki dau'ki fansa laifin waye laifin kine dakin tsaya kunyi bincike duk da ba'a zo wannan matakin da muke kai yanxu ba kuma saida abu ya faru kizo ki d'aga hankalinki cewar bazaki yarda ba duk bai taso ba ha'kuri zakiyi". A zabure Hajiya Khubura tace "wallahi Alhaji bazan yarda tazo har garinmu taiwa 'ya'ya na irin wannan dukan ba saina bita Lagos d'in naci kan uwarta zatasan wace ni nima ba kanwar lasa bace ta ta'bo masifa a kanta" Hajiya Khubura ta fad'a cikin takaici ganin Nadiya zaune a wuri daya har yanxu bata warke ba shine yake 'kona mata rai Abidah ce da batasha duka sosai ba itakam dama bata kwanta a gadon asibiti ba. "A'a Khubura komai ya wuce ta riga ta kad'a d'anta sun tafi a Ina zaki ganta ko Lagos d'in zaki bita"? Ya tambaya yana kallonta yaga wacce amsa xata bashi da mamaki yaji tace "mezai hana nabita har can d'in naci uwarta ita bahar nan tazo ta dakar mun yaran nawa ba dan haka Nadiya tana warkewa zamu shirya muje ko Lagos zata hargitse saina dau'ki fansar dukan nan". "Ban goyi bayan kije ba bana son tada husuma kin manta lokacin auren nace ki tsaya kiyi bincike ne kikece min wanne bincike zakiyi kinsan iyayensa ashe iyayen kud'i ne siyansu yayi suka zo akai auren idan kin tsaya kinyi tunani laifin kine Kuma na tabbata kika bisu Lagos da nufin d'aukar fansa bazaki ta'ba dawowa nan ba sai sun tsafe ki batar dake zasuyi nidai ba ruwana dama na fad'a miki haka batun yanzu ba dan kin 'ki jine amma yanzu Kam kin fahimta ai da kika ga uwar bari". Shiru Hajiya Khubura tai damuwa goma da ashirin wanda take yi danya karfafa Mata gwiwa yace ba ruwansa to taya zata d'auki fansa saidai kawai ta kyalesu Allah ya saka mata Allah ya isa tsakanin ta dasu bazata ta'ba yafe musu ba tana gani Daddy da khaleel suka tafi ita kuma ta koma cikin asibiti. Barinsu gidan ba karamin barazana bane ga Ayrah saboda khaleel ya samu lokacin dazai ri'ka fad'a mata zancen banza da duk abinda yaga dama saidai bai samu cikar burinsa ba duk yadda yaso ta bashi kanta ta'ki ko kad'an bata bashi fuska shiyasa ya samu Daddy akan yana so a saka lokacin bikinsu hakan zaifi masa alkairi idan ta dawo hannunsa amma a hakan nan yana ganinta yana jin sha'awar ta gashi taki amince masa zai iya shiga mawuyacin hali shiyasa ya nemawa kansa mafita tun wuri kafin yaiwa kansa illa Daddy ya tabbatar masa suna kammala school zai d'aura musu aure ko kad'an Ayrah bata sani ba Daddy ba kulata yake ba balle ta sani khaleel kuma ganin yanzu tana da waya yasa bai tareta da maganar tana graduate za'ai musu aure ba saboda tsoron gudun karta fad'awa Aiman ya kira Daddy ya hana a bashi. ***Fara wanka da maganin da Maryam tai humm yadda ta fara cikin nasara haka samari suka ri'ka yimata layi kullum idan ta fita mutun uku hud'u biyar shida sai sun biyota gida lamarin yai mugun damun Mama ganin yadda ake mata layi wanda akai hakan danshi bai ma dawo ba data sani ba'a fara ba saida ya dawo yanzu batasan yadda zatai ba tana ganin saidai su koma gidan me maganin ko akwai wata 'yar dabara da zatai wadannan samarin su daina biyota. Mama tana zaune ita kad'ai a parlor tana tunani har batasan Amaan ya shigo ba duk maganar da yake saida ya ta'bota sannan ta sauke ajiyar zuciya tana kallon sa cikin basarwa dan kar yayi tunanin wani abu tace "Amaan lafiya kuwa naga kamar da akwai abinda zaka fad'a min ko wani abune ya faru"? Kaiya jinjina shima a nasa 6angaren yana sauke numfashi kafin ya d'ago ya kalli Mama data zuba masa ido yace "am Mama dama wata magana zan fad'a miki d'azu Ashraf d'an gidan abokin Abba yace min ranar yazo gidan nan gaisar dake yaga Maryam a lokacin ta shigo yana sonta dan Allah a fad'a miki idan babu kowa nidai nace masa babu duk lokacin daya samu lokaci zaizo" yana rufe baki Mama ta zabura har tana 'kwaruwa wajen cewa. "Yana sonta kuma shi Ashraf d'in ne yace ka fad'a min haka"?. "Eh hakan yace a fad'a muku idan kin amince zai shigo su gaisa Maryam d'in duk yadda sukai shikenan domin bada yaudara yake sonta ba aurenta zaiyi". Kai Mama ta jinjina tana cewa "kuturun ubancan tabd'ijan amma wallahi yaro bashi da hankali uban me Maryam zatai dashi harda wani bada sa'ko a fad'a min? Ya fad'a a banza dan ko Maryam ta rasa masoyi bazata aureshi ba garama karya kuskura naga 'yan 'kafafunsa a gidan nan idan kuwa tsautsayi yasa yazo min gidan nan saina wulakanta shi dan ubansa shid'in banza uwar meya tara a duniya dazai nemi auren mace irin Maryam shashashan banza" ta karasa maganar da 'karfi har kumfan baki take da mamaki Amaan ya zuba mata ido kamar me nazari tambayar dake ransa wanne dalilin ne yasa Mama take fad'a da zage zage dan kawai ya fad'a mata Ashraf nason maryam bayan abun farin ciki ne yayi zaton zaiga ta amshi abun da armashi sai Kuma yaga ta ta'kile shi numfashi ya fitar yana sake d'agowa ya kalleta ganin shita zubawa ido itama yasa yace. "Haba Mama da girman ki kike cewa haka irin wannan maganar ba taki bace Ashraf fa nake nufi d'an gidan abokin abbanmu Abba Ibrahim ko baki gane bane"? Wani irin kallo tai masa tana cewa "ai tunda kace Ashraf na sani basai ka fad'a min kayan takaici ba uwarsa zatai dashi zaice yana sonta ita ba sa'ar auren irinsa bace karya kuskura yazo min gidan nan idan kuwa yazo ubansa zaici". "Kenan yayi laifi Mama dan kawai ya fad'i abinda yake ransa cewa yayifa yana sonta kawai to mene abun laifi anan"?. "Ni a gurina yayi laifi kuma ya fad'i iska ya sota a banza wallahi dan bai isa na bashi auren Maryam ba kome zaiyi ita ba sa'ar aurensa bace tafi karfin irinsa ita saiya canza tasha anan dai bai samu kar6uwa ba". "Ban gane ba Mama taya Maryam tafi karfin aurensa bayan itama mutum ce kamar sa babu wanda yafi wani sai wanda yafi tsoron Allah dukiya basune rayuwa ko jin dad'i ba naga kuma kamar ita kike hange"? Harararsa Mama tai tana cewa "eh Maryam mutum ce bance maka aljana ba amma tafi karfin aurensa ka gane ina nufin bazan bashi aurenta ba kuma kayi min shiru daga haka kar tsautsayi yasa naji ka furta wannan kalmar a gurin alhaji kasan idan magana taje gurin sa kozan mutu sai Maryam ta aureshi kabar zancen iya nan muyi tono mu binne komai a manta da zancen domin hakan bamai yuwuwa bane". "Meyasa zanbar zancen Mama bayan abun alkhairi ne yake bibiyarku amma kuna korewa meyasa hakan"?. "Meyasa zaka bar zancen kake tambaye ta Amaan? saboda ubanka zaka bar zancen ka gane kar nasake jin kayi maganar nan ina gargad'in ka idan tsautsayi yasa ka furta har Alhaji yaji wallahi saina tsine maka gara tun wuri ka kama bakinka" zaro ido waje Amaan yai da mamaki sosai akan fuskarsa yace "Mama meyai zafi tsakaninki da Ashraf haka dan kawai yace yana son Maryam sonta fa yace yana yi kuma dai naga ba wani aibu ne dashi ba kaso masoyinka fa idan ka'ki shi zakaso ma'kiyin ka". Rai 6ace Mama tace "tashi ka bani gu Amaan duk uban da zakiyi Maryam bazata aureshi ba saika ha'kura sannan idan mugun fata ma kake mata itakam bazata auri ma'kiyin taba saidai ta auri masoyinta" mi'kewa Amaan yayi batare daya sake furta koda kalmar aba yabar parlon da harara Mama ta rakashi tana cewa "jimin sokon banza uban me Maryam zatai dashi ga Ahmad jinin sarauta irin 'kasaita zataje tayi zaman aure a gidan sarauta inda mulki da daula suka samu masauki wanda ya fake a inuwarsu maya huta balle Maryam me kankat da zata auri Ahmad gaskiya Amaan yau na yarda baka da hankali anace maka ga gabas kana ga yamma ana ga ruwa kana ga wuta shashashan banza kawai bari zaka dawo ka sameni saina gargad'inka dole saina sake kashe maka warning akan wannan maganar nasan ba hankali ne dakai ba zaka iya idan Alhajin ya dawo ka fad'a masa saidai naji kuna maganar" ta fad'a tana tashi da sauri ta le'ka harabar gida ko yana nan tai saurin fad'a masa kar taje ya tafi office d'in Abbansu yaje ya fesa mai labarin ya jefata a uku ganin babu motarsa harya fita yasa ta dawo ta zauna ita kad'ai sai fad'a take tana zage zage karshe da taga bazata iya ha'kuri ba ta kira Maryam a waya tace tazo yanxu zasuyi magana an samu akasi da akwai matsala gagaruma wacce ta sakosu gaba zaiyi wuya idan zasu iya tsalle wannan damuwar hanya d'aya zatabi dakatar da Amaan shine matakin farko da zata d'auka kafin ta kira Ashraf har gida tai masa tas ta nuna masa 6acin ranta bata goyon bayan Maryam ta aureshi ba matar irinsa bace ya cire idanunsa a kanta. Mama tana zaune Maryam ta shigo ganin yanayinta yasa ko zama batai ba tace "Mama lafiya naga ranki a 6ace haka"? Tsaki Mama taja ta kad'a kai ta ri'ko hannun Maryam ta zaunar da ita a kusa da inda take zaune tana cewa "inafa lafiya Maryam yanzu naji wani abu daya daga min hankali Wai wani shige Ashraf d'an gidan Alhaji Ibrahim ne yake sonki ko a gidan uwarsa ya ganki oho masa to wallahi bari kiji ko tsautsayi zaisa yaxo karkije inda yake idan Kuma kinje kiyi masa mugun wulakancin da takaici zai hana yasake dawowa inda kike ki fad'a masa ba'ka'ken maganganu marasa dad'in ji ta yadda idan ya tafi bazai sake marmarin waiwayar kiba har abada" jin abinda Mama tace yasa ta yamutsa fuskca tana cewa. "Wanne Ashraf kuma a ina ya ganni nidai a tunani na ba had'uwa muke ba balle yace nifa ko fuskarsa yanzu na gani bazan ganeshi ba saboda dad'ewa da mukai bamu had'u ba amma har yace wani yana sona a Ina ya ganni". Cikin takaici Mama tace "koma menene nibai dameni ba sauri zamuyi mu dakatar dashi kafin alhaji yasani kinsan daya sani sai anyi abun nan Niko bana so me laifi ace Humairah yake so bake ba dan kan uwarsa wallahi bazaki aureshi ba idan bazai auri Humairah ba ya ha'kura" ta'be baki Maryam tai tana girgiza kai tace. "Wallahi bai isa ba Humairah ma bazata aureshi ba tunda tana da saurayi me zatai dashi balle ni ina kallon Ahmad kyakkyawan gaske jarumtaccen soja me karfi da kwarjini me zanyi da Ashraf wanda baisan fita filin daga ba baiyi training jikinsa ya murd'e ba kullum yana banki sai kace d'an ministan kud'i nidai bazan auri banker ba garama ya sani ba kud'i nake nema ba sarauta nake so Naga idan zan wuce ana du'ka min ana yabona da yimin kirari ga bayi masu yimin hidima ina tafe ana take min baya wannan shine burina mezanyi da kud'i 'ya'yan banki ina dasu kuma sun wadatar ni tunda nima ba zaman banza nakeyi ba inada sana'a ta balle yace zai rud'e nida kud'i". Murmushi Mama tai harda dagewa tana jinjina kai tace "Yauwa fa karkije gurinsa idan yazo nasan maybe tunda har ya tari Amaan da maganar ki ganshi yazo tunda ba hankali ne dashi ba ya saka mu shiga uku musamman idan akasi yasa Alhaji yana gida ya ganshi yazo d'in kuma yaji ke yake so tabd'ijan heeyyy dan'kari Allah ma ya kiyaye wannan masifa ta samemu domin masife babba ma kuwa da zarar akace yazo shikenan mun kad'e" Cizon yatsa Maryam tai tana cewa "aiko zan nuna masa rashin hankali indai tsantsan hauka ne ya tara ya samu saina tafasa masa jiki da ruwan zafi wallahi saina 'koneshi Allah ya kawoshi ina jiransa zaije yadda ake hauka ganin idonsa". Kai Mama ta jinjina harda cije lips irin muguntar nan ta saki murmushi tana cewa kaji 'yar gari na tabbata kina yi masa haka azaba zatasa bazai sake marmarin zuwa gidan nan koda ziyara bane balle ya furta yana sonki hakan kawai zaki masa idan yazo ki tafasa ruwa me shegen zafi ki lalla6a ki watsawa shege a fuska idan fuskar ta 'kone yai tabo ya samu wacce zata aureshi a cikin nakasassu ko makauniya ko kuturwa amma dai bake ba kekam sai gidan da ake tambari da kakaki inda algaita take tashi wato gidan sarauta" mi'kewa Maryam tai tana cewa "tabbas Mama kin fad'i gaskiya kiran da kikai min kenan zan koma school maybe ma anshiga mana lecture ina nan". "Eh kiran kenan dama abinda zan fad'a miki ne dan kar yayi mana shigar sauri baki sani ba amma tunda kin sani yanzun shikenan naji d'an dama-dama hankalin nawa bai kwanta ba tukuna dai" sunkuyawa Maryam tai tana d'aukar handbag d'inta batare data sake magana ba ta fita Mama kuma ta dau'ki wayarta ta kira Momy taji mene labari akan Ahmad yaya a ina suka tsaya shin yana Shirin dawowa kwana kusa ne su d'au shiri suma ko a'a domin gaskiya itafa ta matsu taga Maryam taje gidan nan matsayin matar Ahmad so take taji tambari da algaitu suna tashi shiyasa bata so abun ya dau'ki dogon lokaci ba'ai ba kar wani akasi ya shigo ciki a fasa". UHMM ALGAITA KUWA ZATA TASHI ZAMU ZO MUSHA BUSA RANAR AUREN NAN MAMA🤣. Nice zanyo gudunmawar ruwan da za'a yayyafawa Maryam idan ta suma🙊 kufa FANS me zaku kawo mata kodan idan kukayi Mata sannu ma ya wadatar😂.............✍️YUSRAH MUSA ABUBAKAR CE. Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë mai tambarin yma dutse Jigawa state. See you tomorrow morning be with me at always my lover's tnks for ur supports we will meet again ina sonku masoya godiya sosai sosai godiya da jinjina gareku thanks you so much I really appreciate it Yusrah ce. 17~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Shakirnah. Bismilllahir Rahmanur Rahim 📿 @YUSRAHMS CE. Page 33 & 34. Bayan sati d'aya Amaan yana gurin aikinsa Ashraf yaje ya sameshi domin su karasa maganar da suka fara yayi sa'a kuwa a lokacin baya aiki yana free zama yayi suna gaisawa cikin sakin fuska ya kalleshi yana cewa "ya ake ciki ne banker ko kud'i ka kawo min yau nima naje na huta da shan shurba"? Dariya Ashraf yai yana cewa "eh abinda yafi kud'i na kawo maka maganar mu nazo mu karasa akan Maryam yaya kukai da ita ko baka fad'a mata ba"?. "No na fad'awa Mama kaje ne"? Kaiya girgiza yana cewa "banje ba ai baka bani amannar naje d'in ba sannan bansan ka fad'a matan ba idan ka amince ko ayau zan iya zuwa muyi maganar da ita". "Ok karka damu Ashraf duk lokacin da kake free kaje ku gaisa ka fad'a mata komai saboda zatafi fahimtarka akan nina sameta na fad'a mata tunda bansan me yake ranka ba shiyasa gara kaje zuwa dakai yafi sa'ko ko"?. Kai Ashraf ya jinjina yana cewa "Eh tabbas gaskiya ne haka ne amma kasan inada matsala na rasa meke damuna haka kawai ina jin tsoron tarar mace nace mata ina sonta ne sai naji wani irin kwarjininta ya kamani" murmushi Amaan yai yana cewa "tab aiko zaka Sha wahala a gurin mace da zarar ta gane kana jin tsoronta shikenan ta samu kofar da zata ri'ka juyaka kamar waina ka daina fad'a ma kar sujika kawai yanxu idan ka shirya koda yaushe ne kaje ku gaisa" kaiya jinjina yana mi'ka masa hannu suka sake gaisawa yana cewa "ok nagode sosai Amaan insha Allahu zanyi kokari naga naje mun had'u zan tafi ka gaida min Mama kafin na samu na 6ulla"?. "Ok insha Allahu zata ji". Shiru Amaan yai bayan tafiyar Ashraf yasan da akwai ya'ki yau indai ya koma gida ya fad'awa Mama shiyasa a take ya yankewa kansa shawara kawai gara yayi shiru idan Ashraf d'in yaje shikenan ai dai sunsan ba shine ya kawo Shiba balle Mama tai fushi dashi yarda yayi da shawarar abinda zuciyarsa ta yanke masa domin hakan ne mafita tunda ya lura Mama ko kad'an batai na'am da maganar Ashraf yana son Maryam ba ya rasa meye dalili amma yasa a ransa zai bincika ya gani. Watan Nadiya guda cur a asibiti sannan aka bata sallama ta dawo gida badan ta warke ba Hajiya Khubura ce to gaji da zaman can din ganin abu ya'ki ci ya'ki cinyewa ana magani kamar ba'a yi 'kafa kullum a kumbure ba sau'ki kuma iya kokarinsu likitocin sunyi sun rasa inda matsalar take a hakan tana iya tad'an dafe wani sanda da suka bata tana tafiya dashi amma ita kad'ai dai bazata iya ba saidai idan ri'keta za'ai kullum tana zaune guri d'aya tunda tafiya wahala take mata ba ranar da zata fito ta fad'i batai kuka ta tsinewa mahaifiyar Sabit ba dashi kansa Sabit d'in daya yaudareta saboda yana so ya aureta ya'ki ya fad'a mata asalin mahaifiyar sa Ashe duk matar da take zarya ba uwarsa bace uwar kud'i ce siyanta yayi yanzu tana kallo babu yadda ta iya da Ayrah saidai ta zuba ido idan Abidah tana yi mata masifa da zagi amma banda ita domin ba wannan ne a gabanta ba damuwarta ta warke kawai shine a ranta. Yauma tana zaune a parlor ita kad'ai babu kowa sai iya khaleel shi kuwa ba'a cikin parlon yake ba yana can gefe kan dinning ya saka bluetooth a kunne sai kad'a kai yake kamar 'kadangare yana murza yatsunsa alamar kid'an yana shigarsa fitowa Ayrah tai a shirye zata tafi school da littafi a hannunta sauri take ma dan taso makara ganinta yasa Nadiya cewa "ke d'auko min ruwa a fridge d'in bedroom d'in mu ki kawo min yanzu karki 6ata min lokaci" kallonta Ayrah tai kamar zatai magana sai kuma ta fasa ta aje book din nata tana shiga part d'in ta d'auko mata ta dawo mi'ka mata tai bata kar'ba ba sai wata harara data sakar mata tana cewa. "Oh bazaki aje ba dole saina kar'ba 'yar isa"? Ajewa Ayrah tai tana shirin d'aukar littafinta cikin tsawa Nadiya tace "ke jaka ki mi'ko min cup mana da uban me zansha ruwan kika aje min zaki tafi wato yanxu rainin ki kika tattare ya dawo kaina saboda kinga ba iya tashi zanyi cikin sauri ba balle na kamaki ko"? Wani irin kallon Ayrah ta aiko mata fuska a d'aure tace "saiki nemi jakar ta mi'ko miki kofi kisha ruwa amma badai niba domin ni mutum ce idan baki sani ba ki sani Ayrah Abdul-Kharim nake da kike maganar dan naga kina zaune guri d'aya ne nake miki haka ina ruwana da zamanki dama nina zaunar dake balle ki huce a kaina tashi kiyi yawonki man waye ya hanaki ina tunanin nan a gidan mijin mahaifiyar ki kike ba'a gidan yari ba balle kice baki da 'yanci sai yadda akai dake ai daman kwad'ayi mabud'in wahala tunda kika bi son zuciya kina tare da nadama Dana sani yanzu kika fara gani sai a gaba ma domin hakkina bazai ta'ba barinku kuji dad'i ba kuma zaki gani" tana fadin haka tai gaba takaici da ba'kin ciki ne suka rufe Nadiya ji take inama ace tana da damar tashi lafiyarta kalau yau babu abinda zai hana ta karyawa Ayrah 'kafa ta fasa mata baki cikin 'karaji tace. "Ke dan kan uwarki dawo min nan idan ki isa"? Batare da Ayrah ta juyo mata tace "na isa harna wuce inda kike tunani amma baki da matsayin da kika isa na dawo miki idan kin matsu dani ki taso kizo ki sameni ina daidai dake" sabon ba'kin ciki ne ya sake kama Nadiya ganin yadda Ayran take tsaye tana jiran taje inda take d'in kuma ta juya mata baya ba ita take kallo ba kamar zatai hauka tace. "Wallahi tallahi bashi kikaci kin d'aukowa kanki masifa da bala'i kin d'ebo ya'ki Allah ya bani lafiya na warke zama saiya gagare ki tsabar dukan fitar hankali dazan nad'a miki a gidan nan ni dake ne" baki Ayrah ta ta'be tana cewa "karyar banza kenan na saba jin irin haka a bakin ki sau tari kuma babu wata tsiyar da kike yi sai kuri dama Abidah ce take ganin damata Kuma itama tunda na goge mata baki a jikin bango take shakkata kodan ke baki sani ba amma yanzu kin sani saura ke yadda na fitar da jini a bakinta kema wadannan ru6a66un hakoran naki sai sun fitar dashi ki jira dawowa ta" Nadiya tana kallon Ayrah ta fita ranta in yayi dubu ya 6aci tana zaune Ayrah ke fad'a mata haka yarinyar da suke cin ubanta take tsoron su amma yau itace take fad'a mata maganganu masu razanarwa da nuna alamar ta fara d'aukar fansa................... Jin 'karar bud'e kofa yasa ta mayar da hankalinta gurin ganin Hajiya Khubura ta fito cikin shiri alamar anguwa zata fita ta kalleta idonta yana kawo hawaye cikin takaici tace "wallahi Umma indai na warke saina kashe Ayrah a gidan nan saita ga ukuba da bala'i zatasan wace ni" dakatawa a kanta Hajiya Khubura tai tana kallon 'kafar tata cike da fargaba tace "metai miki ko 'kafar taki ta taka"? Kaita girgiza tana cewa "ba gara ta taka min 'kafa ba akan irin munanan kalaman data fad'a min wai yaushe kukai sake yarinyar nan ta Raina mutune har take cewa ta gurjewa Abidah baki saura ni". "Au haka tace"?. "Haka tace min harda wani wai minbi kwad'ayi da son zuciyar na auri wanda iyayensa basa kaunata sunci ubana na dawo gida kema ba 'kyale ki take ba yanzu baki da wata martaba da Zaki saka ta abu tayi balle ni banza wacce kashin me gadi ma yafini daraja a gidan nan yanzu" zaro ido Hajiya Khubura tai tana cewa "Wai du Ayran ce me fad'in wannan maganar"?. "Itace man yanxun nan ta fita zata tafi school kinga ruwa nan akan nace ta d'auko min kofi nasha bakiji irin zagin cin mutumcin data ri'ka min ba wai ai tasan babu abinda na isa nayi mata ina zaune a daskare guri d'aya kamar bishiya Allah yasa karna warke Allah yasa 'kafar ta ru6e haka tace min" Nadiya ta karasa maganar tana sakin kukan 'karya cizon yatsa Hajiya Khubura tai tana jinjina kai tace. "Aidai addu'a tai Allah yasa karki warke ko? Humm yau kuwa zan gwada mata rashin imani bari ta dawo wallahi saina saka Abidah tai mata dukan mutuwa ta 6alla mata tata 'kafar itama ta zauna guri d'ayan sannan mu hanata abinci yunwa ta kashe mitsiyaciya bari naje anguwa na dawo wannan case d'in har gaban Alhaji sai yaje yaja mata kunne karta kuskura ta sake miki fatan kafarki ta ru6e idan kuwa bai kulaba zaiga hauka ganin idonsa wallahi sai mun kasheta a gidan nan" ta karasa maganar tana huci saboda yadda ranta yake turiri ta kalli Nadiya wacce ta zubawa kafar ta ido tace "bari na dawo Nadiya ki kula sannan karki damu da abinda ta fad'a indai tsautsayi ya dawo da ita gidan nan da kaina zan jawo miki ita har kusa dake na zauneta kiyi mata tsinannan dukan da zata kasa tashi bari Allah ya dawo dani lafiya itama ta dawo" ta fad'a tana wucewa ta fita duk abinda suke cewa khaleel yana zaune yana sauraron su baice musu 'kala ba har Hajiya Khubura ta fita saida ya gama abinda yake zai mi'ke ya kalli Nadiya yana cewa. "Ke dan ubanki idan Umma ta dawo ki fad'a mata sa'ko na idan tsautsayi yasa ta kawo miki Ayrah kuka daketa na rantse da Allah wannan shegiyar 'kafar taki saina mayar Miki da ciwonta d'anye saina take ta da takalmi na mutsustsu ke ta yadda bazata sake moruwa ba saidai a yanke dama ba 'karyar da kikawa Ayran kenan ba alhali bata fad'a humn zan wakilce ta naci ubanki keda Abidan Allah yasa ku daketa na gani" yana fad'in haka shima ya fita daga gidan aka barta ita kad'ai domin Abidah ma tana school gashi Hajiya Khuburan ma ta fice kuka kawai Nadiya ta kamayi saboda ba'kin cikin hanata taci uban Ayrah da yayi tasan tunda yace haka indai tsautsayi yasa ta daketa ba karamin aikinsa bane ya take mata kafar ya dawo mata da d'anyen aiki tasan ba hankali ya cika ba ga6o ne indai ya fad'i magana ka yarda gaskiya ya fad'a maka bai cika ya fad'i 'karya dan barazana ba................... ***Tunda Ashraf sukai magana da Amaan akan zaizo gurin Maryam bai ta'ba zuwa ba saboda tsoron a yadda zata kar'beshi tunda yasan halinta 'yar rainin hankali ce yana so ya gwada zuwan ya kasa abun na matukar damunsa karshe dole ya samu abokinsa ya fad'a masa matsalar sa shine ya 'karfafa masa gwiwa ya bashi shawarwarin ta yadda zaije mata da yadda zai fara ya tsike ya nuna jarumta kar yayi wani abu da zata gane yana jin shakkar tararta da maganar soyayya yarda yayi da shawarar ya kuma saka a zuciyarsa zaije ya gwada sa'arsa fatansa ta amince masa indai yaga ta amince saboda gudun matsala abun bazai dau'ki dogon lokaci ba za'ai bikinsu kawai hakan shine mafita dayin maganar tasu yakai kusan kwana goma baije inda take ba duk da yace zaije sai daga baya har Mama da Maryam sun manta da wani Ashraf yace zaizo yana sonta kamar a mafarki rana tsaka sai gashi yayi musu dirar mikiya ba sanarwa ba zaton zuwansa ganinsa yasa ran Mama 6aci da'kyar ta amshi gaisuwarsa saboda wani irin damuwa da fargaba daya lullu'be ta domin yau Abban su Maryam d'in yana gida kuma yaga Ashraf d'in harsun gaisa ma saidai baisan me yazo yiba ya d'auka kawai yazo a gaisa ne ta Nan Mama taji d'an dama-dama shiyasa da taga Abban bai fahimci komai ba tayi saurin tashi jiki na rawa ta tafi part d'in su Maryam a lokacin tana zaune tasa waya a gabanta tana kallon photon Ahmad🤔 taga mama ta shiga d'agowa tai da murmushi saboda nishad'in da take ji a wannan lokacin ta kalli Mama ganinta a hautsine yasa tace. "Lafiya Mama"?. Kaita girgiza mata tana waige-waige kamar mara gaskiya tai kasa da murya cikin rad'a tace "ke Maryam yau mun shiga uku zamu tozarta wannan d'an iskan yaron ne yazo"? Cikin rashin fahimta maryam tace "wanne yaron kuma" dan ita ta manta da shafin wani Ashraf ma balle ta damu da yace yana sonta...... "Kefa Ashraf nake miki magana akai yanzu ya shigo muna tare da Alhaji ya gaida mu dad'in da naji ma Allah yasa alhajin bai gane gurin ki yazo ba ya d'auka ziyara ya kawo mana Maryam tashi kije kici kan uwarsa dan babansa kiyi masa kaca-kaca ki wulakanta shi ki wanke min shi tas da ba'ka'ken maganganu ta yadda gaba bazai marmarin 'kara zuwa gidan nan da sunan gurin ki yazo ba dan naga alama indai mukai wasa zai wargaza mana shirinmu da zarar Alhaji ya sani shikenan ya hada mu da masifa dole ki aure ni kuma abinda bana fata kenan Allah ya sauwake miki wannan kaddarar ta sameki" zabura Maryam tai tana cewa. "Wallahi bai isa ba bazan aureshi ko maye ne shi saiya barni wai ana so dole ne"?. "Inaga shi a gidan ubansa ana yi dolen shiyasa ya nace saike bayan ga 'yan Mata nan a gari kamar kayi sannu a baka". "Humm aiko kuwa ya taro masifar da tafi karfinsa wallahi saina sakashi kuka da idanunsa idan bai rabu dani ba". "Kinga Maryam ba magana ba anan mu kad'ai ne baisan kinayi ba tashi zakiyi kije yana can parlon ba'ki ki tabbata kinyi abinda zai 6ata masa rai Wanda zaiji har abada baya so ya sake kallonki ma tashi maza kiyi sauri kafin Alhaji ya sake dawowa tunda mun samu ya fita" mi'kewa Maryam tai a fusace ta dau'ki mayafinta tana fita ranta a 'bace zuciyarta tazo har wuya ta cika dam da fushi burinta tana zuwa ta d'aga hannu da farko ta fara daukeshi da mari kafin ta koro masa munanan kalamai turus tai data shiga ta tsaya tsam ganin da wanda suke tare suna zance harda tafawa suke sun dariya shiru tai tana huci d'agowa sukai duk su biyun suna kallonta ganin yadda Ashraf ya kureta da kallo ji take kamar taje ta rufeshi da mugun duka wani irin ba'kin kallo 'kasan ido tai masa sabida ganin Amaan yana gurin da ace baya nan yau da Ashraf ya gane wacece ita.............. Muryar Amaan taji yace "ke tsaiwar me kike anan tsabar raini tun d'azu kinyi ba'ko baki kawo masa ko ruwa ba balle kizo ku gaisa me kika tsaya yi a part d'in naku kije ki kawo masa abun sha yanzu" kallon amaan dayai maganar tai tana sake jin sabon takaici ya rufeta ko iya bud'e baki ta bashi amsa batai ba sai juyawa datai har hawaye yana zubo mata ta d'ebo masa drinks ta kawo ta wuce kitchen ta had'o masa abinci da kayan cinye-cinye ta dawo tsaye tayi saboda ba zama ya kawota ba hakan ma tsoron Amaan yasa tayi amma yau da ace baya gurin nan parlon nan yayi mata kad'an saboda irin guguwar bala'in data d'auko zata saukewa Ashraf. Mi'kewa Amaan yai yana shirin fita ya kalleta kallo me cike da gargad'i yana jinjina kai yace "ki zauna kuyi magana ta fahimta dashi" kallonsa Maryam tai kamar zata fashe da kuka saboda da yasan yadda take jin tsanar Ashraf d'in nan a ranta da baiso ya nuna mata fuskarsa ba balle harta xauna inuwa d'aya dashi suyi wata magana Amaan yana fita Ashraf ya kalleta ganin bata motsa daga inda take tsaye ba yace.. "Bismilllahi zauna man ba jimawa zanyi ba akwai uzurin dazan tafi nima" wani irin kallo tai masa tana cewa "Ashraf meya kawoka gurina me zakai min mene damuwarka dani meye tsakanin mu da Dole saika shiga rayuwa ta meye had'in biri da kada"? Shiru yai ya zuba mata ido yana kallon ta dama yasan za'ai haka tunda yaga a yadda ta shigo kamar a fusace take kodai bazata amince masa bane domin labarin zuciya a tambayi fuska.......... "Meye ka zuba min ido kana kallona ka amsa min tambaya ina son zan tafi bazama ya kawoni inda kake ba" da mamaki Ashraf ya kuma kallonta yana jinjina kai tabbas bazai samu kar6uwa ba alamar 'karfi tana game 'kiba kalamanta sun nuna masa amsa tun bai furta ba................ Sanyi ne yaji ya shiga ratsa shi dabin jikinsa kallon kayansa yai yaga yadda ruwan juice yake bin farar shaddar dake jikinsa tsananin mamaki ne ya kamashi juice ta zuba masa a jiki kan bala'i bai farga ba ta d'auko miyar shinkafa data d'ebo tana watsa masa a gaban kirjinsa tare ta wulli da kwanon tana nunashi da yatsa fuskarta a 6ace tace "daga yau karka kuskura na Kara ganin wannan jakar fuskar taka ni nafi karfin auren irinka niba sa'ar ka bace ka kama kanka a kaina bana sonka bana son me sonka idan Kuma ana so Dole ka fad'a min da'ki'kin banza jaki wofi ka turo yaya Amaan nace bana so yanxu kuma ka d'ebo kafa kazo gidanmu to bari kaji duk abinda kake ji dashi nafika indai ka sake zuwa gurin na xakaga d'anyan kai sai nayi maka abinda har ka mutu bazaka manta Dani ba banza kawai" mtswww taja zazzafan tsuka tana barin parlon shiru Ashraf yayi yana kallon jikinsa zuciyarsa na tafasa da irin maganganun data fad'a masa tun kafin ya furta yana sonta kamar shi Maryam ta zauna tana wula'kantawa ko bara yazo gurinta ya kamata ta karrama shi balle da kimarsa ta ganshi huuuuhhhh wani irin numfashi ya fitar me zafi da 'kuna tare da mi'kewa yana sake kallon jikinsa yana kuma tunanin taya zai fita ya tafi gida idan ya cire rigar daga Nan Kuma ya fita da ita a hannu karya had'u da Mama ko Amaan su tambaye shi wani abu tuna hakan yasa ya zaro towl karami daga aljihun shi ya goge duk inda miyan ta 6ata masa duk da ba fita yai ba kawai dai ya ragene bud'e kofa yayi ya fita yana fatan Allah yasa karya had'u da kowa yayi sa'a kuwa domin Amaan baya gidan Mama ma bata parlor da sauri ya wuce harabar gida ya shiga motarsa ya nufi hanyar gate yana yiwa me gadi horn yazo ya bud'e masa ya fita ya sani idan yaje gidansu a haka zaisha fad'a a gurin Ummansa dan haka bai nufi hanyar gidan nasu ba ya tafi nasa gidan kawai gara yaje can yayi wanka ya canza wasu kayan inyaso saiya koma hakan zaifi. Humm Maryam kam tana gama fad'a masa wadannan maganganu da watsa masa miya ta fita direct part d'in Mama ta shiga ai kuwa ta sameta sai zaga bedroom d'in take tana goye da hannunta a baya ganin Maryam d'in ta shigo yasa da sauri ta tsaya tana cewa "yaya ya kukai dashi me kikace masa fatan kinyi abinda bazai dawo mana gida ba ko"? Kai Maryam ta jinjina tana cewa "kwarai nasan har abada bazai manta da hakan ba shiyasa na Kona masa rai zuwa nayi na tarar da ya Amaan acan ya sakani na d'ebo drinks da snacks nakai masa Wai hakan bai isaba saina dad'o Niko na d'ebo masa shinkafa na d'ebi Miya da yawa a kwano ina ganin ya Amaan ya barmu mu biyu na d'auke kofin dayasa na xuba masa juice a ciki na kware masa shi a kansa sannan hakan ma da naga bai gamsu ba na dau'ki miyar itama na watsa masa ita a jikin farar shaddar sa sannan na fad'a masa munanan kalamai marasa dad'in ji nasan yanzu kam shikenan dole xai barni bazai sake waiwayata ba" kai Mama ta jinjina tana sakin murmushin jin dad'i da farin ciki tace "yauwa 'yar albarka naso ace kin had'a masa harda mari dan yasan da gaske ba sonshi kike ba amma hakan ma ya fahimta komai ya wuce". "Komai bai wuce ba Mama kinsan zai iya idan yaji gida uwarsa ta gani yace nice ita kuma ta fad'awa mahaifinsa daga Nan magana ta dawo gurin Abba na shiga uku nasan ya Amaan ma saiya kusa kasheni dan duka shiyasa gara naje gidansu har gaban gyatumar tasa na sake masa masa warning dan tasan d'an nata bai samu kar6uwa ba yaje can ya nemi daidai dashi ya aura". "yauwa shikenan ma hakan zakiyi karshen abun kenan maza jeki kar lokaci ya 'kure mana idan kin dawo mayi maganar a nutse itama uwar tasa idan ta kawo miki rainin wayo ki mata tsiyal zagi irin na tsamar nama zakiyi mata indai ta shiga safgarki ki nuna mata ita tsohuwar banza ce bata iya haihuwa ba 🙊". "Ok Mama bari na dawo" ta fad'a tana juyawa ta fita motarta ta d'auka kanta tsaye babu wata fargaba kojin tsoro taje gidansu har lokacin Ashraf bai koma ba yana can gidansa Ummansa na zaune a parlor taga Maryam ta shiga ti'kas ti'kas babu ko sallama taje har gabanta kamar zata rufeta da duka ta ri'ke 'kugu tana cewa "kece mahaifiyar Ashraf ko? Kodan basai na tambaya ba da gani babu tambaya ai ga kamanni nan na gani to bari kiji ba zama ko tambaya ya kawoni ba zuwa nayi na fad'a miki idan d'anki ya dawo ki fad'a masa ya fita daga gonata niba sa'ar aurensa bace nafi karfin auren banza irinsa karya kuskura na sake ganinsa a gidan mu idan tsautsayi ya sake kaishi zanyi masa abinda har abada bazai manta dashi ba ki fad'a masa sa'ko daga Maryam kiyi masa albishir cewa abinda nayi masa yau wanda zanyi masa a gaba sai yafi wannan muni" tana fad'in haka ta juya fuuu ta fice da kallo Hajiya Rabi'atu ta bita cike da tsananin mamakin wace wannan yarinyar meya had'a su da Ashraf itafa kamar naso ta gane wacece ita kamar Maryam d'in Hajiya Halima kodai itace? (Abinda yasa bata santa ba saboda iya mahaifin Maryam da mahaifin Ashraf ne suke abota amma su a junansu ba ruwan kowa da kowa shiyasa Hajiya Rabi'atu batasan Maryam bace kawai kama tagani ta gane) kaita jinjina a ranta tana cewa "Kai babu wata tantama itace amma meya had'a su me Ashraf yaje yi gurinta tazo min har gida tai min fitsara bari ya dawo naji aiko indai yace min sonta yake kafin ya rufe baki saina daukeshi da mari yadda tazo ta tsiyata ni d'in nan wannan yarinyar bata da tarbiyya bata gaji arziki ba" mi'kewa tai ranta a 'bace ganin bazata iya jiran dawowar saba gara ta kirashi yazo taji meye ya had'asu dan bazata sake d'aukar raini irin haka ba yanzun ma jira take ta kirashi taji indai bashi da laifi tayi mata haka har gida zataje taci uban Maryam d'in domin ita mace ce me zafi ba'a kawo mata raini...............Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë. See you tomorrow morning Be with me at always my lover's. TYPING 📲Wed, Apr/9/25 7:56AM YUSRAH MUSA ABUBAKAR 🤘💯. 👑 ROYALTY 👑 (Girman sarauta _ 'yan sarauta) WhatsApp no:+234 816 098 3083 Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë. ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫 Home of hospitality and harmony gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan ta. S*W*E ✍️Yusrah Musa Abubakar Maman Fatima Zarah Elham little Zarahn Aunty Momyn Ashraf. 18~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil hafizinah. Bismilllahir Rahmanur Rahim 📿. @YUSRAHMS CE Page 35 & 36. Lokaci ya wuce da yawa kwana da tashi asarar me rai tafiyar Ahmad yau shekarar biyu cis baizo gida ba ko kad'an su baby har sunyi graduate sun d'ora sabuwar makaranta Shadad shima yazo gida sau d'aya yaga su Mami yana komawa kuma dama saura shekara d'aya ya kammala degree d'insa shikenan ya dawo gida ya bud'e babban company wanda yake juya gwala gwalai da sarrafa su amma a wannan karon ma yazo zaiyi azumi saboda sun samu hutu sai bayan sallah shima Ahmad da sukai waya da Momy yace mata wannan shekarar a gida zaizo yayi azumi su Baby tunda sukaji haka suke shirye shiryen zuwansa da taka tsantsan tun kafin ya dawo kowa ta shiga taitayinta ranar da aka fara azumi na farko sunyi tunanin zasu ganshi sai sukaga shiru haka washe gari ma har dare babu labarin sa kullum zuba ido suke su ganshi har akai goma baizo ba kasa ha'kuri Baby tai suna zaune tare a parlon Momy take cewa. "Nikam Momy na tambaye ki man Yaya Ahmad koya fasa zuwa azumin ne"?. "Nima ban sani ba Baby saidai ki tambayi Abdul-Hamid ko sunyi waya dashi ya fad'a masa ya fasa amma meyasa kika tambaya"? Gyara zama Baby tai saboda tasan baya nan tace "Momy naga har anyi goma bai zo bane shiyasa nayi tunanin ko fasa zuwan yayi"? Kallonta Khairat tai cikin tsokana tace. "Au marmarin zuwansa kikeyi kenan kamar wanda zai kawo miki abun dad'i kodai kewarsa kike"? Gwalo ido waje Baby tai tana cewa "naji kewar wa tabd'i na rasa wanda zanji kewarsa sai ya Ahmad uhm amma dai fad'a kike dan dad'in baki ko"?. "A'a ba fad'a nake ba da gaske nake miki maganar ba wasa nasan meye a ranki tunda zuciya ba ganinta ake ba".. "Uhmm babu abinda yake raina sai alkhairi". "Ai dama alkhairin ake so kuma nima alkhairin na fad'a ni dama nafi son idan zuwan ma zaiyi yazo baki a bud'e lokacin mun koma school aidai mun rage zaman gida ba kamar yanxu da kullum muna nan idan ba'a same mu a gurin Momy ba za'a ganmu a gurin Mami ko 6angaren su Sultan kinga kuwa ai bamu huta ba ka sayar da akuya tazo tana goga maka danga idan kuwa muna school saifa lokacin da muka dawo". "Haka ne to Allah yasa ma sai bayan sallar zai daw....................... Jin 'karar tafiyar takalmi yasa Baby bata karasa ba tai saurin juyawa tare da Khairat lokaci guda suka zaro ido ganin Ahmad ya shigo sanye da kayan soldier fuskarsa a rufe da facemask duk 'kamewa sukai musamman Baby data tabbatar yaji maganar da takeyi kuma yasan a kansa ne gashi yayi musu gargad'in karya sake jin sunyi murna akan tafiyarsa, tsaye yayi ya zuba musu manyan idonsa wanda tsoro yasa babu wacce jikinta baya rawa a cikinsu kaiya jinjina batare dayace musu komai ba ya juya ya fita daga parlon saboda Momy bata gurin ta jima da tashi ta shiga part d'inta . Babu wacce bata sauke numfashi ba a cikinsu ganin ya fita baice musu 'kala ba maybe zuwa zaiyi ya cire Kaya ya dawo mi'kewa baby tai tana kallon Khairat tace "please Aunty Khairat dan Allah taso mu bar part d'in nan mu tafi gurin Sultan Sharfaddeen kafin ya Ahmad ya dawo wallahi idan har ya dawo yadda ya jinjina kan nan sai mun kwana namu kan yana ciwo kinsan ba ruwansa da azumi mukeyi idan yaga damar cin ubanmu" ta karasa maganar tana mi'kewa itama Khairat d'in tashi tayi saboda tasan abinda Babyn ta fad'a gaskiya ne bazai duba azumi ne a bakinsu ba indai yaga dama saiyace zai hukunta su shiyasa ma suka nemarwa kansu mafita suna shirin fita Momy ta bud'o kofa tana cewa. "Ina zuwa haka a cikin wannan ranar"?. "Gurin Sultan zamuje ziyara". "Amma duk da baku tashi zuwa ziyarar ba sai yanzu da tsakar rana haka kodai bakwa jin azumin yau d'in ne"?. "Eh Momy badan son ransu zamuje ba akwai dalili ne". "Wanne irin dalili"? Kamar Baby zata kuka gudun karya dawo ya samesu tace "laifi mukaiwa ya Ahmad".. "A Ina kukai masa laifin bayan baya nan". "Ya dawo fa yanzu ya shigo part d'in nan ko kayansa bai cire ba". "Ok ya dawo amma har kukai masa laifi daga dawowar tasa". "Su6utar baki nayi Momy bansan yana kan hanyar shigowa ba nace Allah yasa karya dawo sai bayan sallah ina fad'a najishi a bayana shiyasa daya jinjina kai ya fita nacewa Aunty Khairat mu tafi gurin Sultan kar da azumin nan ya bamu wahala koya saka mu watering a rana" murmushi momy tai tana fitowa ta zauna tana kallon su tace "ok sai kun dawo ku gaishe min dasu" tana rufe baki wuf sukai waje har rige rigen fita suke amma me can nesa suka hangoshi da alama shima inda suka nufa ya tafi humm ba arziki suka juya da gudu suna yin part d'in Mami ko tsayawa a parlor basuyi ba tana magana ma inaaa basu jita ba hankalinsu yayi gaba da gudu suka fad'a bedroom d'in su suna sanyawa kofar lock kowa tana fitar da numfashi kallon juna sukai suna dariya baby dake dafe da 'kirji tace. "Kai Allah ya tsare mutum ya zama kamar wani dodo a riga gudunsa" zama Khairat tai tana cewa "toda meye idan ba dodon ba tunda tsoronsa muke yi Yaya Abdul-Hamid aiba haka muke masa ba sannan Yaya Shadad koke kinsan ba haka muke masa ba aidai shine ma za'a ce yana da zafin rai irin na ya Ahmad d'in amma ai yana sake mana muna zama muyi hira dashi harda dariya idan kinga fushinsa ko d'aure fuskarsa saikin yi masa laifi shi kuwa boss Ahmadi me zamani fa"? Dariya baby tai itama tana zama tace . "Wa yaga Ahmadi humm idan tsokanarsa kike sonyi saidai kice Amadu inaga yafi kayan haushi akan kice masa Ahmadi ga wanda kika 6ata sunan sosai zaifi d'aukar zafi" gwalo ido Khairat tai tana cewa "ni kaza mijina zakara ban shirya cin sallah da tabo a jikina ba". "Aina d'auka a shirye kike uhm Allah yasa dai bamuyi masa laifi ba dan nasan idan yaga ya neme mu ya rasa d'in nan ma sai yace munyi gudunsa ne nidai har asha ruwa bazan koma part d'in Momy ba saidai idan barci zamuyi bari ma kiga nad'an kwanta na matse kafin a kira sallah" ta fad'a tana hayewa gadon kallonta Khairat tai tana murmushi batace komai ba kuma ita bata kwanta ba sai tuna diramar su kawai take tana dariya gasu da tsoro ga son suyi gulmarsa. Koda dare basu yarda sun shiga part d'in Momy akan lokaci ba saida suka tabbatar daya gama zamansa yabar part sannan suna rarra6awa suka je suka kwanta washe gari kuwa suna yin sallar asuba suka sake guduwa part d'in Mami sukai kwanciyarsu acan suka koma barci har wajen sha d'aya da rabi Khairat ce ta fara tashi tabar Baby a kwance saidai ta tasheta tace mata wanka zatai itama ta taho gurin Momyn shiyasa Khairat d'in tayo gaba tayi sa'a ita kad'ai ce kamar yadda tayi fata babu kowa zama tai tana gaida ita daidai Momy ta amsa idon Khairat ya sauka akan wani basket da aka 'kawata shi da ado cike da burgewa tace. "Kai Momy wannan kyakkyawan basket d'in na waye gaskiya ya tafi dani wallahi ki ganshi d'an kyakkyawa" ta fad'a tana shafa jikinsa saboda yadda yake d'aukar ido yana she'ki kallon basket d'in Momy tai tana cewa "na Baby ne" baki Khairat ta bud'e tana qara kallon Momy da mamaki tace "na Baby kuma waye ya kawo mata nasan dai bata da saurayi waye to ya bata"?. "Ahmad ne". Da sabon Khairat ta zaro ido tana cewa "ya Ahmad kuma ya bata Ramadan basket tofa kyauta ya bata kenan ko kuma me"?. "Eh kyauta ya bata man zai bata aro ko ajiya ne"?. "Amma Momy ina sai budurwar ka kake baiwa ko har 'kanwa kana iya siyawa meyasa ya sai mata nasan dai wannan irin kyautar saurayi da budurwa ne amma ita kuma ya bata saidai idan da wani abu ko"?. ''Jeki tambaye shi meyasa ya bata domin nima ban sani ba shi kuwa ya sani zai baki amsa". "A'a basai na tambaye shiba azumi akeyi karna jawa kaina sambad'a da rana tsaka na kasa kaiwa magriba kawai a barshi nasan maybe ra'ayi yayi ya bata matsayin sa na yayanta". "To kinsan da hakan kike tambaya"?. "To ai Momy abunne da mamaki indai matsayin 'kanwa ya bata meyasa ni bai had'o dani ba"? Murmushi Momy tai tana kallon Khairat tace "nasan dai keba 6angaren karatun jarida kike yiba amma kin iya tambayar 'ka'ka uwaka ta haifeka ina Babyn take yanzu"?. "Tana part d'in Mami wanka na barota tana yi itama nan d'in zata taho". "Ok tazo ta d'auke abunta" kawai shine abinda Momy tana tana mayar da hankalinta wani wurin daban shiru Khairat tai ta zubawa basket d'in ido tambayoyi ne masu yawa a ranta saidai tasan batada amsar su kuma bata da wanda zata tambaya ya bata amsa saidai Ahmad shi kuwa ko a buge take idan ta ganshi saita nutsu balle tana cikin hankalinta so take tasan meyasa Ahmad zai baiwa Baby Ramadan basket sonta yake ko kuma ra'ayinsa ne kawai yasa ya bata anya kuwa babu wani abu ta sani masoyi ne kad'ai ke haka indai ba sonta yake ba to me yake kaita girgiza a fili tace "ina sam ba haka bane wannan tunani nane kawai taya hakan xata yuwu" batasan a fili tai maganar ba saida taji Momy tace "meye ba haka bane"? Numfashi ta sauke tana saurin dawowa cikin nutsuwarta jin zatai 6arin zance tace "ba komai Momy bari naje na kira Babyn tazo ta bud'e mana muga mene a ciki". "A'a ki 'kyaleta basai kinje ba saurin me kike zata zo ai duk abinda yake ciki zaki gani har ki gaji" Momy na rufe baki Baby ta shigo da sallama tana zama tace "wash Allah na wallahi kamar banyi wankan nan ba tsabar azabar da nake ji daga part d'in Mami kafin nazo nan har ruwan jikina ya bushe zazzafar iska ta fara buguna gaskiya da alama axumin yau da'kyar zan kaishi" dariya Khairat tai tana kallon ta tace "ai indai zakiyi wankan wuri to kuwa dole azumi ya baki wahala saka ruwa a jiki yana qara wuyan azumi idan baki sani ba". "Humm aiko da alama yau zanci ubana dad'in abun ma ba wani abu zakai ba daga sallah sai kwanciya shiyasa nake tausayawa kitchens wallahi ga azumi ga zafin wuta ga aiki uhmm Allah sarki" ta fad'a tana girgiza kai kallonta Khairat tai tana cewa. "Baby kalli wani basket" Khairat ta fad'a tana nuna mata kallonsa tai tana zaro ido cike da burgewa tace "wow wannan kyakkyawan basket d'in daga ina ko Yaya Shadad ne ya aiko miki shi daga can gaskiya ya had'u sosai"? Dariya Khairat tai tana cewa "A'a wacce ni me ido bad'an ciki ha'kori ba sakata wannan yafi karfina naki ne". Sak Baby tai tana kallon Khairat tace "nawa Kuma ni waye xai bani Ramadan basket ba saurayi gareni ba tsokana ta kike ko Aunty Khairat saboda kinga babu me bani shikenan nima Allah ya kawo min habibty na kafin wata shekarar idan ya kawo min na rama nayi miki dariya tunda nima yanxu dariyar kike min" Kai Khairat ta girgiza tana cewa "ke Baby Wallahi da gaske nake naki ne haka Momy tace" da mamaki Baby ta nuna kanta tana sake kallon basket d'in tace. "Nawa dai waye ya bani"?. "Yaya Ahmad ne" Khairat na rufe baki Baby ta zabura idonta kamar zai fito waje tace "wanne Yaya Ahmad d'in amma dai bana gidan Nan ba"?. "Na nan gidan man shine ya baki kuma ki tambayi Momyn kiji idan ni baki yarda dani ba ko kina ganin tsokanar ki nake yi" kallon Momy Baby tai jiki a sanyaye muryarta ma da sanyi tace "wai haka Momy dan Allah kice aunty Khairat tsokanata take" yadda tai maganar yasa Momy sakin murmushi tana d'an girgiza kai tace "ba tsokanar ki takeyi ba Baby da gaske take Ähmäd ne ya kawo min d'azu yace idan kin shigo a baki Ramadan basket d'inki ne injishi tun daga can ya taho miki dashi". Dafe 'kirji Baby tai tana cewa "a bani kuma mene had'ina da Ramadan basket Momy inace sai idan kana da saurayi ne yake baka irin wannan ko"? Kai Momy ta d'aga tana cewa "eh haka ne". A razane baby tace "toni kuma meyasa ya bani"? Dariya Khairat tai tana cewa "kika sani ko kema hakan take abu a duhu a 'kulle a ba'kar leda waye yasan dashi sai wanda ya ajiye ta yuwu kema hakan yake nufi". "Hakan yake nufi me? please Aunty Khairat daina fad'a karkisa zuciyata ta buga ko cikina ya hautsina wallahi yanxu ma bakiji yadda nake jina ba gabadaya zufa ce take zuba min a jikina kiyi shiru haka". "Akan me zanyi shiru Baby kuma tsaya na tambaye ki idan a misali da gaske yace yana sonki aurenki zaiyi fa kinsan dai da aure a tsakanin ku to nan kuma ya zakiyi kinsan dai dole ki auresh..............saurin rufe mata baki Baby tai kamar zatai kuka tace "dan Allah Aunty Khairat ki daina fad'a wallahi har naji kinsa hankalina ya tashi gani nake kamar da gaske komai ya faru taya ma za'ai ya Ahmad zaice yana sona zai aureni hum'um wannan labari ne kawai ko a mafarki bazai yuwu ba" dariya Khairat tayi ganin yadda tasa Babyn ta susuce tace "ke nima da wasa nake miki kawai dan naga yadda zakiyi ne wai kiga idonki dan Allah duk kinbi kin burkice". "Toba dole na burkice ba Aunty Khairat naji kina neman d'ora min wani babban nauyi a kaina aure nida Yaa Ahmad dai Allah ya rufa asiri bana fatan hakan ko a mafarki" kallon kofar shigowa Khairat tai tana cewa "humm lallai kam Ya Ahmad wai nayi shiru kawai abar maganar kar ayi irin ta jiya yazo ya kamamu muna gulmarsa yau kam bazai Mana uzuri ba kuma kinga Momy ma bazata sa baki ba saboda tasan mune bamu da gaskiya". Ita dai Momy tana jinsu Bata tanka ba har sukai suka gama abinsu ganin baby ta manta da wani maganar basket Khairat tace "please Baby duba mana basket d'in nan mugani mene a ciki" kallon basket d'in Baby tai kamar bazata ta ta'ba ba sai kuma tasa hannu a hankali ta jawo shi gabanta tana kwance 'kyalle da aka d'aurawa kwandon akayi shi kamar gift🎁 yaye karamin kyakkyawan towel d'in dake kai tayi wani irin daddad'an kamshin turare ne ya bugeta bud'e hanci Khairat tai tana cewa. "Kai wannan kam 'kamshin turaren ya Ahmad ne wallahi sauri ki fito mana da kayan Baby na matsu naga meye da meye a ciki idan dana d'auka mu d'auka" ta fad'a tana dariya uhmm ita dai Baby batace komai ba sai kayan ciki data fara fitowa dashi hijab da carbi da littafai su 'kawa'idi ahlari da al-qur'ani da arba'una hadis su muftahul ibadat harda wani kyakkyawan d'an karamin littafi an rubata d'an musulmi a jiki sai turare da roban dabino da zamzam ganin wani abu me kama da gidan wasi'ka📧 da Khairat tai yasa tasa hannu tana d'aukowa tace.. "Mene wannan Baby baki duba mun gani ba kamar wasi'ka cefa bud'e mana"? Ta fad'a tana mi'ka mata kar'ba Baby tai tana bud'e bakin abun ta d'auko wata farar takarda a ciki tana bud'ewa da sauri Khairat ta matso cike da gulma suka fara karantawa cikin mamakin abinda suka gani a rubuce kamar haka. "I SEE THOUSAND GIRLS I KNOW HUNDRED GIRLS I TALK TO TEN GIRLS AND I LOVE ONE GIRL ya rubuta haka da manyan ba'ki sai yayi babban love💓 a karshen rubutun sannan yaja layi ya sake rubuta Zuhra Ashraf Sharfaddeen Ramadan Kareem (A-Z) a kasan gurin yasa Sultan Sharfaddeen family rufe baki Khairat tai idonta kamar zai fito waje dan mamaki tace................................✍️ YUSRAH MUSA. TOFA ME KHAIRAT ZATACE ANAN?....... WANNE IRIN YANAYI NA TASHIN HANKALI KUKE TUNANIN BABY ZATA SHIGA BAYAN KARANTA WANNAN LATTER?........... KUNA TUNANIN BABY ZATA YARDA DA CEWA AHMAD NE YA RUBUTA WANNAN ABUBUWAN?.... WANNE IRIN RUD'ANI ZATA SHIGA?................. SANNAN MEYE ZAI BIYO BAYA?. Duka domin samun amsoshin wadannan tambayoyin ku kasance dani YUSRAH MUSA ABUBAKAR Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë 🌺. Yma dutse new world Jigawa venture's. 😘Be with me at always😘 Mai so har 'karshe should DM me kuyi min magana ta WhatsApp number na zaku samu complete d'insa akan naira na gogan naira har naira d'ari biyar😂 insha Allahu ina marhabun da kowa. WhatsApp no: +234 8160983083 #500 Ac no: 2410673902 Ac nm: Yusrah Musa Zenith Bank. ME KAMAR SARKI #300 MINISTER ASHRAF #300 SAFREEYYAH #400 Masu bukatar wasu littafan nawa zaku iya samu ta wancan WhatsApp number nawa insha Allahu ina maraba da kowa. YMA DUTSE NEW WORLD 🌏.