[2/13, 4:43 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writtin by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writter Asso*☀️ *shafi na ɗaya* Wani irin kuka take mai tsuma zuciya kai dagajin kukan kasan irin kukan nan ne wanda yake tasowa daga karkashin zuciya, ba kowa ke gane mai kakeji ba sai wanda yataɓa irin kukan"Yah Mus'af mai nake gani da gaske ne?dan Allah kagayamin ba gaskiyya bane wannan katin dana gani bana gaske bane kace karya ne" gaba ɗaya yayun nata dasuka zagayeta ba wanda yai magana wanda ta kira da Mus'af kasa yayi da kansa yana kwafa, kallo ɗaya zaka masa kasan ran maza yaɓaci saboda tsananin ɓacin rai yama kasa magana, Mami da batasan abin dake faruwa ba futowarta kenan daga ɗakinta da shirinta natafiya wajan aiki da sauri ta karaso wajan su inda taga yaran nata gaba ɗaya a tsugunne sun saka Aimanah a tsakiya "Mansur maiya farune kuka zagaye Aimanah lafiya?" da sauri wanda aka kira da Mansur yaɗago batareda yayi magana ba ya nunawa Mami katin hannunsa yamaida kallonsa kan Aimanah dake kuka har sannan kamar ranta zai fita, Mami da sauri ta lalubi kujera mafi kusa ta zauna saboda wani jirine yaɗebe tai luuu zata faɗi kaɗan yarage taje kass tasoma ambaton "Innalillahi wa'inna ilaiheer raji'un ban gargaɗeku akan maganar nan ba Muneer bakuji abinda nafaɗa ba" Adakile Mas'ud yafara magana ransa ɓace "Mahh mufa bamu muka gaya mata ba da abinta ta shigo gidan nan" "Ku bani waje, ke Aimanah zonan" "Mah yanzu dan Allah shi..."Kamun shuru Mus'af" mami tafaɗa a tsawace ranta ɓace, fuuu Mus'af yafice daga falon kamar yana shirin tashi sama Mansur Yakalli Manneer yace "Bi yaron nan ban yarda dashiba kasan halinsa" da sauri Muneer yafita Mas'ud yakalli agogo yai tsaki yafice. Ma'aruf yakama hannun kanwar tasa yamikar da ita tsaye yakaita wajan Mami, kanta taɗora saman cinyar Mami tana cigaba da kukanta "Yi shuru Aimanah daina kukan muyi magana, nasani nasan abinda kikeji please daina dan Allah" "Mahh nayi shuru kike cewa fa?"Katin ɗaurin auran Al'Mustapha nagani, yanzu Murja tabani shi a kofar gida har tana gayamin maganganu marassa daɗi" "Naji daina manta dashi" "Mahh daman daina zuwan da Mustapha yayi fasa aurena yayi shine kukaƙi gayamin gaskiyya kuke faɗamin yakoma jordan ashe yana kasar nan Mah mainayiwa Mustapha ya yaudare ni har haka?" "Baki masa komaiba Aimanah lamarine ya canza" Ammi ke faɗin haka wacce tashugo falon yanzu fuskarta cunkushe da damuwa, a kasa ta zauna tareda wurgar da makullin motarta da handbag ɗinta, hawaye yafara zuba a idanunta tana kuka sosai "Anty yaya zanyi ina zansa rayuta yanzu ya zanyi afasa auran nan Amarya ta cuceni wallahi nasan ba haka tabar Mustapha ba harni Mai sunan manya zai kalla yace min nayi duk abinda zanyi amma baizai fasa auran Sumayya ba" rushewa takuma yi da kuka tareda haɗa kanta da jikin kujera "Saudat yakike so nayi ina kuke so nasaka raina, kuka yana maganin matsala ne?"Baya maganin komai ke kuka Aimanah kuka dame kukeso naji kubarni naji da kaina dan Allah" "Kuka bashi zaiyi magani ba gaba ɗaya ku manta da komai kuyi addu'a ke Aimanah bar wannan kuka kona ɓallaki haba duk kinbi kin tasar mana hankali saboda Mustapha yafasa aurenaki Mustaphan shine autan maza" afusace Aimana tamike fuuu tawuce ɗakinta gado tafaɗa taci gaba da kukanta son rai anan barci yayi awon gaba da ita mai cikeda mafarkan Mustapha. *Anty Amarya Home* "Murjana ku kula da abubuwan nan sosai banaso asami matsala kisaka su a karkashin gadon idan kun gama jera komai, ki kula sosai kada su Hajiya Luba sugani kinsan dai wahalar damuka sha kafin a juyo da hankalin Al Mustapha kan Sumayya" "Nasani Mama nafasan komai kuma zan kula da komai ba abinda zai faru, haba nabari akaga wannan layun ai bancika jininki ba Mama" "Yawwa guda liyata Nasani nakuma yarda dake shiyasa nasako ki acikin wannan tafiyar banda ma auranku ya haramta da Mustapha ai daman da bashida mata saike"Sumayya ta haɗe rai tana hararar Amarya "Kai Amarya nimafa zan iya"dariya kawai mama Amarya tayi tamike ta futa can falon ta inda yan uwanta suke shirin tafiya gidan Mustapha yiwa Sumayya jere, sai da suka fito tsakar gida da gayya Amarya tasaki guɗa tafara rawa tana wake wakenta, Ammi mahaifiyar Al Mustapha dake ɗakinta tana jiyo guɗar Amarya ranta yakuma ɓaci zuciyarta tai wani irin kunci hawaye suka zuraro daga idaniyarta kamar ta share amma zuciya taɗebeta ta fito afusace tana gafda fita daga ɗakinta Ahmad ɗanta na biyun dake tsaye a falon yana zagaye yace "Ammi dan Allah karki kulata kibarta da halinta neman abokin yi take kuyi atafi dake abaki ana faɗar bakida kirki wasuma suce bakin ciki kikeyi da auran ɗanki" "Ahmad nabari fa kace in tsaya ina kallo anamin cin kashi akan ɗana, ɗan dana tsugunna na haifeshi amma arinkamin gadara afaɗa mana daman ai ba farin ciki nake da wannan auran ba yaje ya yaudari yar yayata sannan nayi farin ciki da nasa zaɓin Mustapha zai gani in..." "Kidaure karki yiwa Yaya baki Ammi kimanta da komai kiyi addu'a, nagama maki shirin barin gidan nan kutafi saudiyya kuyi umara keda Aimanah ku ruki Allah akan wannan al'amarin na tabbata wannan aikin asiri ne kigafa irin soyayya dake tsakanin Aimanah da Mustapha amma yanzu ko maganar ta bayaso ayi masa" "Ahamad saima kaga Aimanah yau tabani tausayi sai yau taji labarin auran nan bakaga yanda hankalinta yatashi ba, harna baro gida tana barci" "Nasan za'ayi haka shiyasa Alhaji Mansur yace kar asanar mata naji daɗima daya kasance yana gari hakan ta faru yace abuja zai wuce da ita" Ammi bata tanka ba ta koma ciki duk da har sannan tana jiyo maganganun Amarya tanata sakin habaici Alhaji Kamal tsaye a ɗakinsa yakasa zaune yakasa tsaye kallon kanin nasa kawai yake yanda yaketa zuba alawa biskit da goro cikin babban kwali afusace Alhaji Kamal yake magana "Sadik nizaku tozarta? nace ba hannuna a ɗaurin auran nan amma kashige gaba kunason jonyo matsala tsakanina da amini na? da wacce fuskar zan kalli prop wanda muka gama tsaida ranar auran Mustapha da Aimanah dashi?" "Da fuskar da kaje kanema masa auran Mustapha shiya zo yace maka yanason Aimanah yanzu kuma yadawo yace yanason Sumayya to mene aciki za'ayi masa auran dole ne namiji ne fa shi kabawa Alhaji Faruok hakuri kawai yarinya tanemi wani Allah baisa Mustapha mijinta bane" Alhaji Sadik yana gama faɗar haka yafuce da goransa da alawa a kwali batare daya kalli inda Alhaji Kamal yake ba. Aimanah ko bayan data tashi daga barci alwala tayi ta gabatar da sallar la'asar da akayita tana barci addu'o'i tayi sosai sannan ta fito babban falon gidan, shuru ba kowa sai fanka da T b dake kunne suna faman aiki shuru tayi tazurawa tibin idanu tana kallo azahiri zakace kalon take amma a baɗini tunani take irin soyayyar dasukai da Al Mustapha Alhaji Umar Farouk mai naira hafaffan garin kano ne a karamar hukumar Ɗanbatta wani karamin kauye dake karkashin ɗanbatta local govement mahaifin Alhaji Farouk ba fulatanine yanada arzikin shanu kaji zabbi akuyoyi da tumaki Farouk shine ɗansa guda ɗaya tak daya haifa hakan yasa bakaramin so yakewa Farouk ba, birni yakawo sa anan yayi karatun sceoundry bayan ya kammala yatafi A b u zariya acan yayi digiri yai masters ɗinsa, yadawo cikin garin kano da zama kasuwanci yafara kafin daga baya yafara koyarwa a jami'ar bayaro dake cikin garin kano, yahaɗu da matarsa Hajiya Aisha anan garin kano sukai aure shekera guda ta haifo ɗanta namiji ranar suna aka saka masa Mansur Aisha irin matan nan ne masu haihuwa duk shekara hakan yasa kafin shekaru shida auransu ta haifo yaranta maza biyar Cif Mansur ne babba Muneer Mas'ud sai Mus'af da Ma'ruf daga nan ta saida haihuwa ta koma karatu tazama cikakkiyar likitar mata tana aiki asibitin nasarawa, Bayan wani lokaci tahaifo kyakkyawar yarta budurwa yarinyar datasha gata wajan yayunta maza ba kamarma Mus'af wanda yaɗau son duniya yaɗorawa babyn da tun randa aka haifeta Ya Mansur dake ajin karshe a makarantar scoundry yasa mata suna Ummu Aimanah suke kiranta da Aimanah, Alhaji Farouk yanada babban aboki Kamal wanda sukai A b u zariya tare babban abokinsa ne kuma amini tare akai bikinsu da Farouk ya auri Asiya haihuwarta biyu duka mata anan gidan Farouk Alhaji kamal yaga kanwar Aisha Saudat ba ɓata lokaci akai auransu ta tare gidansa inda yake zaune da matarsa, Asiya da Saudat zama suke na amana bakajin kansu wata tara Saudat ta haifo santalelan ɗanta namiji aka saka masa Mustapha bayan wani lokaci Alhaji kamal na zaune da matansa da yaransa guda shida Asiya da Saudat zama suke na amana ba'ajin kansu atsakaninsu baka banbance wancan ne ɗan wancan gaba ɗaya yaran nasu ɗaya suka ɗaukesu suna kiran Asiya da Momy Saudat kuma Ammi, wata rana Alhaji Kamal sunje taro Katsina shida Alhaji Farouk anan yaga Naja bayan wasu satittika aka ɗaura auransa da ita yakawota cikin gidan sa yahaɗeta da matansa daga farko zaman nasu abin sha'awa sai daga baya Naja tafito da wasu halaye na rashin mitumci bata ragawa kowa a cikinsu hakan yasa suka tattara ta suka ajjeta gefe suka rungumi yaransu, Mustapha yana kammala scoundry ɗinsa kanin babansa Alhaji Sadik yatafi dashi jordan inda yake aiki, acan yayi karatunsa na gaba da scoundry harya fara aikin banki har sannan bai dawo nageriya ba yana can saidai waya, sosai suke zumunci da yaran gidan Alhaji Farouk waɗanda suka dungule suka zama zuri'a guda Mas'ud da Mustapha sa'anine abokai kuma komai nasu tare, scoundry ɗaya sukayi koda Mustapha yakoma jordan abotarsu bata rabuba kullum suna tare a waya, Aimanah ta taso cikin yayunta masa masu matukar kaunarta kowa burinsa ya kyautata mata gata suke bata ta ko'ina saidai gatan dasuke nuna mata baisa sun bari ta sangarce ba daga tayi ba dai daiba zasu sata a gaba suyita mata faɗa da nasiha har zuwa sanda ta girma ta zama yammata saiya zamana komai suka samu na Aimanah ne ba kamar ma Yaya Mansur daya zama babban mutum yafara aiki a wani gidan talvision dake nan garin kano, Albashinsa na farko Aimanah yakashewa su saida Alhaji Farouk dasuke kira da Daddy yayi masa faɗa tareda nuna masa ya tattala kuɗinsa yasamu yasai fili yafara gini kafin ya fara neman aure, ko ina Aimanah zataje ya Mus'af ke kaita kasancewar duk yayun nata sunada motocin hawa, yau Aimanah tun safe take ɗoki zataje gidan yaya Mansur da'akayi bikinsa watanni uku dasuka wuce bata taɓa zuwa gidanba matar yayan Mansur tana yawan kiranta yaushe zatazo takawo masu ziyara in tace zataje sai Mus'af yace bazataje ba Yaya Muneer ne yau yamata alkawarin ta shirya zai kaita, ɗoki take sosai tana dawowa daga school tayi wanka ta shirya sai dai har la'asar yayan baidawo daga kasuwa ba duk tabi ta damu tasami Mah aɗakinta bayan ta gaidata tace "Mah Yaya Muneer har yanzu baidawo ba yayimin alkawarin zai kaini gidan Yah Mansur najisa shuru ki aramin wayarki na kirasa" Mah batace komai ba tazaro dubu ɗaya sabuwa cikin jakarta tabawa Aimanah "gashi nan shiyace nabaki bazai dawo da wuri ba an kawo kaya yana store ana saukewa idan yatawo zai kira Anty Ummin saiki futo titi ku haɗu" da ɗokinta ta amshi kuɗin tana tsallan murna ta fita tana faɗin "Mah saina dawo" Mah murmushi tayi tareda faɗin "Allah yakiyaye hanya" Aimanah tajima bakin titi tana jiran abin hawa amma bata samuba saboda walahar abin hawa da'ake fama dashi a wannan lokacin, harta fara shirin komawa gida tana kokarin tsallaka titi mota ta faka a gabanta murmushi tayi da sauri takarasa wajan motan ta buɗe murfin motan ɓangaran mai zaman banza murfin motar tarufe tajuyo tana murna "Ya Mas'ud ina zaka na jima anan ina jiran..." wanda tagani zaune wajan mai tuki yasa tai saurin katse maganar datake tana zaro idanu😳cikeda tashin hankali tasoma magana "Afuwan malam nashugo maka mota kai tsaye nayi zaton motar yaya Mas'ud ce" ɗaure fuska wanda ke zaune a wajan tukin yayi yana cigaba da tukinsa cikin kwanciyar hankali da kwarewa "Malam magana fa nake ka ajjeni" "Na ajje ki wayace kishugo motata kin shugo kenan daman ina neman kan mutane kungiyarmu sun bukaci kan mace daga nan wajan yanka zan kaiki abani kan na wurgar da gangar jikin ko nabawa karena ya cinye" "Innalillahi wa'inna ilaiheer raji'un kataimaka ka ajjeni su Yaya Muneer zasuyi kuka suna sona sosai" wayansa ce tayi kara yaɗaga kiran yana dariya bataji abinda akace ba a wayar amma abinda yace ne yasata buɗe baki "E ina hanya gani nan na ɗakkota nan zan kawota wajan yanka a gyara wukaken nan"........✍🏻 07039793439 [2/13, 4:43 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Associations*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na biyu* A tsorace tasoma kokarin buɗe murfin motar amma motar taki buɗuwa hannayanta ta haɗa waje ɗaya alamar roko "Dan Allah bawan Allah kabuɗemin na fita wallahi na tuba bazan sake shiga motar kowa ba kataimaka kaji tausayi na in koma gida inna koma bazan sake futowa ba ko makarantama na daina zuwa" Lumshe ido yayi tareda buɗesu tarwai akan fuskarta azahiri fuskarsa turɓune take ba alamar fara'a amma a baɗini dariya ce fal cikinsa ganin yanda gaba ɗaya hankalinta yatashi alamun tsoro karara sun bayyana a gareta, "In sauke ki? In saukekifa kika ce na rantse bazan sauke kiba sai munje inda muka nufa" Kuka tasaki tareda ɗora hannunta aka tana karanto Innalillahi wa'inna ilahir raji'un tsabar kiɗimewa da tsoratan datayi har batasan an karaso gidan Yaya Mansur ba, ganin anbuɗe murfin motar yasa ta fita da sauri tana waige waige, motar yaya Mansur ta hanga a harabar gidan ita ta tabbatar mata da tabbas gidan Yayane da gudu ta kwasa zuwa ciki kamar zata tashi sama ta faɗa falon gidan bako sallama, "Innalillahi Anty Ummi ɓoyeni a ina zan ɓuya ɗan yankan kai ne ya satoni" Anty Ummi dariya take sosai ganin yanda duk tafita a hayyacinta ta firgice "Zo nan Auta bafa ɗan yankan kai bane Mustapha ne fa ɗan Ammi baki gane saba?" wata ajjiyar zuciya ta sauke tai saurin zama saman kujera taci gaba da ajjiyar zuciya har sanda Yaya Mansur suka shigo tareda Mustapha, Aimanah ta ɗaga kai tana kalon Mustapha da Anty tace mata ɗan Ammi ne inbata mantaba ai tasan Al mustapha babban yaron Ammi wani dogo fari marar jiki yaza'ayi ace wannan shine, wannan kakkauran mai murɗaɗɗan jiki shine Mustapha kai sam hakan bazata yuwuba, ita dai bata yarda ba jefi jefi tana yawan kallon Mustaphan wanda shima itan yake yawan kallo insun haɗa idanu yasakar mata murmushi itako ta harareshi ta ɗauke idanunta har zuwa sanda Yah Muneer yazo ɗaukarta su koma gida. Wasa wasa saiga zazzafar soyayya tashiga tsakanin Mustapha da Aimanah wata iriyar soyayya mai zafi ko yaushe suna tare a gidan Mahh harta kai ga manya sun shuga ciki kowa yayi murna da wannan haɗin, Aimana tana gama scoundry Mustapha yabiya mata tayi jam, jam ɗinta tayi kyau sosai hakan yasa tasami gurbin karatu a jami'ar B u k tamaida hankalinta sosai kan karatu musamman daya kasance Mustapha alokacin yakoma Jordan sunyi nisa da juna amma ko yaushe suna tare a waya suna kashe juna da kalamai masu daɗi da sanya shauƙi ko yaushe suna bege da mararin ganin juna dasan kasancewa tare a karkashin inuwar aure, Mustapha gaba ɗaya zaman Jordan ya ishesa hakan yasa yatattaro yadawo kano gaba ɗaya da aikinsa, kusancin dasuka samu yasa soyayyar su takara karfi hakan yasa iyaye suka tsaida lokacin aure, kwatsam cikin hakan Mustapha gaba ɗaya ya ɗauke wuta daga zuwa wajan Aimana hakan bakaramin tasar hankalinta yayi ba tadamu sosai ko wayarsa ta daina shiga ta tambayi Mahh ina Mustpha tace mata yakoma Jordan aikin gaggawa yasa aka kirasa shine yasa tafiyar ba shiri...Aimanah tayi nisa sosai a tunani har bataji maganar da Mah ke mata ba, Mah cikeda damuwa ta zauna kusada Aimanah "Aimanah dan Allah ki daina damuwar nan kisa aranki daman Mustapha ba mijinki bane kimaida hankalinki kan karatunki kinga kina fenal year namiji kudan zumane kimanta da damuwar sa ki dubi gobenki kimanta da jiyanki" "Mahh shikenan shikenan narabu da Mustapha bazan aure shiba"... "Ke dayallah kimana shuru wai akanki aka fara hakane zaki tsaya kina yima mutane kuka" Mus'af ke faɗar hakan a hasale kamar yakai mata duka "Kuma kizama cikin shiri gobe zakubi jirgi karfe goma keda Ammi zuwa saudiyya" Mama Amarya shagalin biki tasha sosai a gidan daga ita sai kawayanta da ƴan uwanta dasuka zo daga katsina, ango sai nan nan yake da amarya Sumayya wacce yakeji nan duniya bayada sama da ita, gaba ɗaya gidan ba wani shaƙiƙi na Mustapha kowa yakama gabansa cewarsu bazasu tsaya suga kayan takaici ba, Yayunsa mata na gidan aure kuwa fatan alkhairi sukayi tareda cewar bazasu zo ba, Ahmad da Shaheed ƙannansa ba wanda yaje wajan ɗaurin aure gaba ɗaya kowa haushin Mustapha yakeji, Mama kaɗai ke tausaya masa kusan itace kan komai nasa na bikin, da daddare karfe takwas aka kai amarya gidanta dake nan jikin gidansu Mustapha Alhaji Kamal ne yabasa gidan tun lokacin daya dawo Kano da zama. Aimanah maida hankali tayi sosai wajan addu'a da rokon Allah yacire mata son Al Mustapha ya mata zaɓin alkhairi, sosai takejin haushin Musty yanda ya yaudareta yaje ya sami wata ya aura, ta kullacesa sosai a zuciyarta sosai takejin haushin maza da tsanarsu a zuciyarta aganinta duk halinsu ɗaya, satinsu biyu a saudiyya suka dawo nageria a Abuja jirgi ya saukesu Yaya Mansur dake zaune acan da iyalansa shiyaje ya ɗakko su daga filin jirgi, washe gari Ammi tabi jirgi zuwa kano Aimanah Yaya Mansur yahanata komawa ganinsa inta zauna anan ɗin zata kara samun nutsuwa, tanajin daɗin zama da Anty Ummi dayaranta maza guda biyu, kullum tana cikin ɗaki bata wani sakewa a gidan nusamman yanda su Anty Ummi keshan soyayyar su gaban kowa, har yanzu bata koma nomal ba wani iri takeji sam jiki da zuciyarta sun kasa sabawa da rashin Mustapha takanyi kuka sosai tana yawan kiran lambarsa bata shiga tayi kuka tayi addu'a harta gaji, yau tana zaune a ɗaki karatun kur'ani take a wayarta karar buɗe kofa dataji yasa tai saurin ɗago dara daran idanunta tana kallon kofar dan ganin mai shugowa Anty Ummi ce shirye cikin doguwar rigar atamfa mayafinta a hannu "Sannu Amaryar ɗaka, kindai kasa daina tunanin Mustapha" "Anty kin rigada kinsan komai kinsan irin soyayyar danakewa Musty irinta ba lokaci ɗaya take fita a zuciyaba inajin soyayyar Musty ita zata kaini kushewata" Anty Ummi cikeda tausayawa ta zauna kusa da Aimanah tabbas kamar yanda tafaɗa ne tasan komai tasan zazzafar soyayyar dake tsakanin Mustapha da Aimanah bata misali bace soyayyace mai cike da kauna da aminci dole idan ɗaya ya rasa ɗaya manta sa zaiyi wuya, bata taɓa zaton akwai wani abu dazaisa Mustapha ya juyawa Aimnah baya ba yaje can ya auri wata tabbas da walakin wai goro a miya dawata a kasa ba Hakanan Mustapha zai guji Aimana ba ita tini tafara zargin akwai sa hannun Amarya matar Alhaji kamal a lamarin "Yi hakuri Aimanah yanzu tashi ki rakani nayiwa su Zayyad siyayya gobe Monday zasu koma makaranta muyi maza mu dawo kafin su dawo daga islamiyya Zaheed yace saiya bimu kinsan baida daɗin tafiya" "Anty da kinyi tafiyarki insuka dawo gidan bakowa bazasuji daɗi ba kinga leena bata nan" "Bazan tafin ba dake zamuje kin maida kanki matar ɗaka duk ba rigimar nan nikan Musty bai kyautaba daya canza mana Aimanarmu daga rigimammiyar mai yawan fara'a zuwa wannan mai taurin kan, oya maza maza tashi ki shirya mu fita nabaki minti biyu" Aimanah batan tasoba ta shirya cikin doguwar rigar abaya, sakar egypt hular net tasa a hanta kana ta naɗa ɗan karamin mayafin abayar akanta tana kokarin saka glass a idanunta wanda yazame mata jiki kusan ko yaushe kaganta tana sanye dashi a idanunta, bakaramin kyau yake mata ba, Anty Ummi data sake dawowa ɗakin jin shuru Aimana bata fito ba sak tayi tareda faɗin "Wow My Aimaah kinga yanda kikayi kyau" "Anty Plese kidaina faɗar sunan nan Aimaah bansaba ba daga bakinsa kaɗai nakeson jin sunan nan faɗar sunan yana daɗa tadamin mikin dayake cikin zuciyata" Aimanah tafaɗi haka miryarta na rawa kamar zata fashe da kuka "Ok bazan sake faɗar sunan ba amin afuwa kar ayi kukan nan yaɓata mana wannan special kwalliyar, Allah yasa mu samo wanda zai biya kuɗin kwalliyan nan" murmushi kurum Aimanah tayi ta zura plate shoe tafice zuwa wajan ajje motoci na gidan. Amota Anty Ummi nata tsokanarta saidai kawai tayi dariya taci gaba da danna wayarta har suka karasa babban kantin siyayya Aimanah tasoma fita daga motar kafin Anty Ummi tafito suka jera zuwa ciki. Ahankali yake tukin motarsa cikeda nutsuwa da kwarewa karatun kur'ani yake sauraro acikin motar yanabi ahankali jefi jefi yana murmushi shi kaɗai yabuga sitiyarin motar ahankli kallo ɗaya zaka masa kasan yau yana cikin zallar farin ciki, harya gifta shoprite yayo baya kaɗan yayi parking cikin wajan yafuto ya kulle motar yashiga ciki "Kai Anty Ummi kalli wancan atamfa yayi kyau sosai bari na ɗakkowa Mahh nasan ma nason jar kala" batajira mai Antyn zatace ba tayi gaba takai hannu zata ɗakko shiya yakai nasa da sauri ta ɗauke hannunta wanda shima hakan yayi saboda wani shoking da hannun nasa yayi sanda ya haɗu dana Aimana atare suka ɗago suna kallon juna kusan tare suka furta "Sorry" jin sun faɗa tare sai abin yabasu dariya shi yaɗan dara sosai itako Aimanah murmushi kawai tayi tamaida hankalinta wajan ɗakko atamfar, shiko gefe yakoma yana kallon Aimana yanajin wani iri a xuciyarsa karo na farko kenan daya taɓa jin irin haka a rayuwarsa ta nan duniya sake gyara tsayuwa yayi yana cigaba da kallonta duk inda ta motsa baiyi aune ba yaga tana shirin barin wajan "Ji mana yammata nace Dan Allah kozaki zaɓar min atamfa da lace zanyi tsaraba" har tayi kamar bata jiba komai ta tina kuma saita juyo ta kallesa kallo ɗaya ta ɗauke ganinta daga kansa tamaida hankali wajan zaɓar abinda yace saita ta kai hannu zata ɗauki wani lace kawai taji bakinta ya furta "Uwa mata ko kanwa?" Sarai yagane tambayar amma saiya basar yai kamar baijita ba yaci gaba da danna waya "Nace ba ina tambayya banida lokaci fa" "Namaki kala da wanda yake da mata tayar mota ne ni haka kuma banda kanwa" maganar daya faɗa ta fitar da amsar tambayarta hakan yasa taci gaba da zaɓar kaya saida ta ɗauki Lace huɗu atamfa uku mayafai sannan ta ajje masa a gabansa taci gaba da tafiya da sauri yabi bayanta da kayan shirim a hannunsa yai saurin zuba kayan a cikin basket ɗin datake turawa "Wannan kayan da kika ɗiba yayi yawa banida kuɗin dazan biya duka" "Bakada damuwa ni ina dasu indai harka ta iyaye ce bama sanya musamman ma mahaifiya ita ɗin ta musammance" murmushi yayi yabi bayanta ganin tasoma tafiya zuwa wajan biyan kuɗi inda ta hangi Anty Ummi tsaye da alama tagama siyayyarta ita take jira, Aimanah na kokarin ciro Atm card ɗinta cikin jaka shi kuma ya ɗakko nasa daga aljihu yamikawa ma yaron dake wajan "Ga siyayyanmu nan ta ɗauki kuɗin duka" yafaɗi haka yana ajje masa kayan saman canta, Aimanah tayi saroro tana kalon gayan mai karfin hali "Kaga ba tafiyarmu ɗaya karɓi ka ɗauka anan iya nawa saika ɗauki nasa a card ɗinsa" "Madam kiyi hakuri narida na shigar" cashiar ɗin yafaɗi haka yana cigaba da danna computer ɗin dake gabansa, aka gama haɗe kaya ko wanne ledarsa daban gayan shiya bikaci hakan ta hanyar ware kayan data basa daban da wanda ta ɗiba, Aimanah a fusace tayi gaba bata tsaya ɗaukar ledar ba Anty Ummi ita ta haɗa da nata ta ɗauka tanayiwa mutumin godiya hartayi gaba yace "Anty in wani bai rigani ba kibani phone number na kanwar taki" Anty na murmushi ta gaya masa lambar ya loda cikin wayarsa tareda save na number yana tsaye a compount na store ɗin yana kallonsu suka shiga mota sannan shima ya shuga tashi yana murmushi ahankali ya furta "Fenally yau dai Momy tayi sirika yau zanje Jigawa da daddaɗan labari....✍🏻 07039793439 [2/13, 4:43 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation Shafi na Uku Jiki a sanyaye yake tuka motar haka kawai yau yakejin ransa ba daɗi damuwa da baisan ko ta macece ba duk tabi ta addabi zuciyarsa haka kawai yaji baisan komawa gidansa amma ba yanda zaiyi dole yakoma, badan ransa na soba yakama hanyar zuwa gidan, tun daga falon gidan ranshi yakuma ɓaci wani uban kauri daya jiyo daga kicin yasa yai saurin nufar kicin ɗin abincime ake dafawa yakone yayi baki kirin sai hayaki yake gaf yake da kamawa da wuta da sauri yakashe gas ɗin ya sauke tukunyar kasa, jingina yayi da kantar kicin ɗin yadafe kansa yana faɗin "Ya salam" azafafe yafito ya kalli ko'ina kaca kaca komai zaman kansa yake kudaje sai bin falon suke dafe kansa yayi ganin ko kayan dasukai break ba abinda ta ɗauke yana nan ajje a wajan, afusace ya banga kofar ɗakin nata ya shiga amma duk zafin daya ɗakko sai yaji tayi masa wani gingirim tsoro da shakkarta suka shigesa yaji yama kasa faɗar abinda yazo faɗa, asanyaye ya zauna gefan gadon datake zaune sai faman latsa waya take da alama chat take kasa yayi da kansa kana yace "Yanzu Sumayya kina kallon yanda gidan nan yake amma kike zaune anan kina chat gaba ɗaya gida kaca kaca dan Allah in kikayi baki bazakiji kunya ba" zumburo baki tayi gaba tareda karkata ɗaurin ɗan kwalinta tana harararsa tace "Aikai kajawo nace maka kasamo mana mai aiki kace bazaka kawo ba basai kayita kallo ba kazanta yanzuma aka fara, ni katashi ka yo mani take away kunya nakeji kuma bazan iya dafa abincin ba" wani kallo yayi mata kamar bazaije ba amma data ɗago ta kallesa ba shiri yamike zai fita saboda wani tsoronta daya shigesa da sauri yafice daga ɗakin yana waiwayanta, amota ya zauna tai shuru yana tinani ahankali yatada motar tasa bai tsaya ko ina ba sai office ɗin abokinsa kuma ɗan uwansa Mas'ud, Mas'ud dake zaune cikin office ɗinsa yana danna laptop yaɗago ya kalli Mustapha daya shigo abirkice bako sallama haka yasami waje ya zauna, Mas'ud ya tura laptop ɗinsa gefe yaja tagumi yana kallon Mustapha dayai wani zuru zuru kamar mara lafiya maganar Mustapha ta katsewa Mas'ud kallon dayake masa murya a raunane Mustapha yace "Mas'ud na canza ko naga kanata kallo na wai dan Allah nima mutum ne?" aɗan tsorace Mas'ud yasake kallon Mustapha jin maganar data fito daga bakinsa "Mutum ne kai mana maiya faru kake wannan tambayar?" "Gaba ɗaya banida nutsuwa Aboki wani iri nakejin kaina gani nake kamar bani ba" "Aboki anya kuwa kanada lafiya ko asibiti zamuje a duba ka?" "Bazamu ko ina ba lafiyata kalau kawai kamin addu'a kagayawa Ammi tayafemin nadaina zuwa gaisheta idan natafi gidan sai naga gaba ɗaya na rasa hanyar" "Mustapha kana azkhair kuwa anya ba aljanu ne suka shigeka ba, kayawaita azkhair sosai sannan kana karatun kur'ani koda yaushe kana sakawa a redion cikin motarka" wayar Mustapha datayi kara tasa ya mike da sauri yafice daga office ɗin, Mas'ud yabisa da kallon tausayawa tabbas bako tantama asiri ne ajikin Mistapha inko har hakane tabbas zaiyi tsaiwa daka wajan ganin yataimakawa abokinsa, yazama dole yaje yasami Ammi suyi magana. Sumayya ta fito daga ɗakinta tana waya dariya take sosai harta shiga kicin da sauri ta karasa gaban tukunyar dake ajje a kasa ita gaba ɗaya ma ta manta data ɗora girki, da sauri tamaida murfin ta rufe saboda wani kauri daya bigeta ta maida wayarta kunne taci gaba da magana da mamanta Amarya "Amarya aiki yayi kyau sosai ai kirawa boka tsito kuɗi bakiga yanda Mustapha kejin tsorona ba komai nace yayi jiki na rawa yakemin kawai dai maganar yar aikin nan ce dai yaki yadda ki gayawa tsito yayi aiki dan Allah ya amince nasami mai aikin nan, kinsan dai ni Mama ban saba da wahala ba ko gidam Innah ba abinda nake saida agama naci nabar kwano nan bare wannan gidan mai uban girma bazan iya aikin saba wallahi Mama" "Ke dayallah raguwa kina nan kina kazantarki ko tabbas ki canza inba haka ba zamu sami matsala dake duk abuna bana zama da kazanta, sannan maganar kuɗin nan kisake masa magana boka ya tabbatarmin zai bayar yau in aka tambayesa yaɗaure masa baki" "To Mama zan tambayesa yanzu dai na aikesa siyomin abinci" "Sumayya abinci kuma mai zanji wannan abu ba daɗin ji ke bazaki girka ba kenan gaskiyya ki canza koda asiri fa saida kissa wani abun ke tafiya dai dai adaina siyo abincin nan kina dafawa kinfa rigada kin iya komai nida nakeso ki rike zuciyarsa ta yanda koda asirinmu ya karye yaazama akwai wani abu naki da saboda shi kaɗai zai iya zama dake" "Mama yakike wannan fatan ai bazai ma karye ba muda muke da boka tsito ai bamuda sauran matsala zama daram a gidan Musty nifa Mama sai yanzu ma naji ina son sa da duk kwaɗaita min daular da kike bana hangowa sai yanzu danake cikinta" shigowar Mustapha yasa ta katse kiran. *AIMANA* tagama shirinta na kwanciya ta kwanta kusada Zaheed tana gyara masu blanket wayarta tayi kara hannu tasa saman bedsite drower ta ɗauki wayar tata ganin bakuwar lamba ba suna yasa ta ajje harta katse bata ɗaukaba sau biyu ana kira bata ɗauka ba sai ana ukun ta ɗaga kiran tareda karawa a kunnanta "_Amincin Allah yatabbata a gareki ya tauraruwa a cikin taurari_" dim taji gabanta yai wani irin faɗuwa ta ciro wayar daga kun nanta ta kalli screen ɗin taga sam batasan lambar ba batama taɓa ganin ta ba "Afuwan ba wannan layin kake nema ba" "Shi nake nema mana Hayatie yakike ya daran?" tsaki taja takashe wayar gaba ɗaya tayi addu'ar kwanciya barci ta kwanta da hannun dama rufe idanunta tayi bayan tayi bisimillah ahankali tasoma rero karatun suratul mulik har barci yayi awon gaba da ita. Abbas ganin ta katse kiran yayi murmushi ya fito daga ɗakinsa zuwa na Hajiyarsa, Hajiya Hafsatu mahaifiyar Abas na zaune cikin bedroom ɗinta tana duba littafin addu'o'i na hislum muslim ɗagowa tayi tareda amsa sallamar gudaliyar ɗannata murmushin fuskarta ta faɗaɗa haɗi da faɗin "Malam Abas bakayi barci ba nazaci gajiyar hanya zata saka kayi barci da wuri" "Hajiyata ina zan iya barci banzo munyi hira ba gaba ɗaya aikin nan baya barina sakewa dake sosai kamar da, Hajiya kinsan me?" "Bansani ba Malam Abas saika faɗa" "Hajiya kinyi suruka" Abas yafaɗi haka yana sunkuyar da kansa alamar jin kunya "Nayi farin ciki sosai Malam Abas Allah yasa albarka yatabbatar mana da alkhairi" "Amin" yace ahankali yakarasa gabanta ya tsugunna yaɗora kansa saman cinyarta "Hajiyata kimin addu'a yarinyar nan tasoni fiyeda yanda nake sonta Hajiya nafaɗa sosayayya mai zafi kowane bugu na zuciyata yana bugawa da soyayyatar ta" Hajiya Hafsa na murmushi tadafa kan yaron nata tana masa addu'a, ba sabon abu bane a wajansa tun yana yaro haka take masa harya saba indai yanason wani abu yakan tsugunna a gabanta yace "Hajiya amin addu'a" ba ɓoye ɓoye a tsakaninsu komai yana iya faɗa mata baya shayi ko shakkar faɗa, Hajiya Hafsatu wayayyar maca ce tana matukar son ɗannata guda ɗaya tak da Allah yabasu itada mijinta Alhaji wada idiris, Hira sosai Hajiya da Abas suke har zuwa sanda Alhaji Wada yadawo Abas yabar ɗakin bayan sun gaisa da Abban nasa...✍🏻 Game bukatar shuga group ko gyara ko wani karin bayani 07039793439 [2/13, 4:43 PM] +234 904 746 4048: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GMAOuujeP6dLtFTHo1Edxx 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation Shafi na Huɗu Ahankali take karanta addu'ar tashi daga barci, idanunta nakan agogon bangon dake manne jikin bangon ɗakin, karfe biyar saura na asuba sakkowa tayi daga kan gado ta shiga bathroom ta ɗauro alwala jin anata kiran sallah raka'anun fijir tasoma yi bayan ta idar ta zauna tana addu'o'i kafin sanda taji anyi assalatu, ta tayar da sallah, tasbihi tayi bayan ta idar da sallar tasoma karanto azkhair na safiya, harta kammala sannan ne Zeeyad yatashi tana kallonsa yashuga bathroom yaɗauro alwala yatada sallah, tamike tareda ɗauke daddumar datayi sallah akai ta linke ta maida ta ma'ajjiyarta, tashin Zaheed tayi ta taimaka masa yayi alwala shima yai sallah wanka tamasu ta gama masu shirin makaranta sannan suka fito, lokacin bakwai saura Leena suka tarar tagama shirya kayan breakfast bisa danning ta koma kichin, Aimanah tana zama ta tina da wayarta ta kalli Zeeyad tace "My Son ɗakkomin phone ɗina a ɗaki" yamike a nitse ya tafi, dai dai sannan Anty Ummi da Yaya Mansur suka sakko daga sama, Aimanah tagaidasu cikeda ladabi, tare sukayi break fast gaba ɗaya bayan sun gama Yaya Mansur ya wuce wajan aikinsa tareda yara zai ajjesu a school, Aimanah tana buɗe wayarta sako na shugowa kamar daman jira ake ta buɗe wayar _Amincin Allah yatabbata a gareki tauraruwata fatan kin tashi lafiya, Dan Allah inaso abani dama na kira wayan nan muyi magana bakon masoyi ne,_ Bakon masoyi Aimanah tafaɗa a fili batareda tasan ta faɗa ba Anty Ummi dataji abin data faɗa dariya kurum tayi taci gaba da danna wayarta, minti kaɗan tsakani wayar Aimanah tayi ring kamar bazata ɗaga ba ganin lambar da'akai mata tex ce yanzu, saida ta kusan katsewa sannan ta amsa kiran kara wayan tayi a kunnanta tai shuru batace komai ba "Haba kyakkyawata kika kashe wayanki jiya" "Malam mai yasa kake da naci ne bani kake nema ba, wannan ba lambar da kake nema bace nagaya maka tun jiya, Dan Allah kadaina kirana kana takuramin" "Uhm uhm ke nake nema ba kece jiya muka haɗu a shoprite ba kika bani lambarki?" dariya Aimanah tayi kana tace "Kaine wai ina kasami lambata?" "Sirri ne amma ki tambayi Antynki" "Anty Ummi" Aimanah ta faɗa ahankali "Indai itace wacce kuke tare jiya to ki tambayeta, Aimanah tsaya ki saurare ni dan Allah nazo da lamari mai girma agareki Anty Ummi tabani labarin soyayyarki da Mustapha da tambarin da kika yiwa maza, ki sani kamar yanda mata ba halinku ɗaya ba haka maza muma ba halinmu ɗaya ba, ina sonki so irin so na aure bada wasa nazo ba dan Allah kibani dama naje ga iyayanki su bani damar zantawa dake mu fahimci juna manya su shiga a tsaida ranar auranmu, niba yaro bane bazanyi soyayya irinta yara ba" "Soyayya kuma daman har yanzu akwai wannan kalmar, ni babu ita a wajena, a zuciyata da wajena tuni an kashe so" Aimanah na gama faɗar haka ta katse kiran ta ajje wayar ta wuce ɗakinta da sauri, Anty Ummi tabi Aimanah ta kallo tana girgiza kanta hannu tasa ta ɗauki wayar Aimanah dake ring sun jima suna magana da Abas daga karshe tamasa kwatancan gidansu Aimanah dake kano. Abas bashida kowa daya sani a kano hakan yasa yasha wuya sosai kafin yasamo gidansu Aimanah da Yaya Mus'af sukayi magana ya nema masa izinin ganin Aimaha Daddy yace yabasa dama yaje inhar sun dai daita zaiyi farin ciki da hakan, cikeda ɗoki Abas ya ɗauki hanyar Abuja baishiga garin da wuri ba lokacin dare yayi goma saura na dare hakan yasa kawai ya wuce gidansa, cikeda takaicin rashin shugowarsa garin da wuri,kasancewar washe gari lahadi shiyasa dayayi sallar asuba yakoma barci bai tashi ba sai sha biyu na rana, yayi mamakin irin baccin dayayi "Barcin gajiya" yafaɗa ahankali yana murmushi shi kaɗai, wanka yayi haɗeda ɗauro alwala yafito, tsab ya shirya cikin Sky blue ɗin yadi ya fita masallaci, ahanyar dawowarsa daga masallacin ne yakira wayar Yaya Mus'af bayan sun gaisa ya bukaci yabasa adress na gidan Yaya Mansur yasan koya kira Aimanah ba ɗagawa zatayi ba yana tinanin ma tasa lambar sa a blacklist sabida jiya yayita kiran layin baya tafiya, Ya Mus'uf yabashi adress bayan sun gama wayan ya kira Yaya Mansur yamasa bayani Abas da abinda zai kawosa gidan, Mansur yayi farin ciki sosai duk da daman Ummi ta gaya masa haɗuwar su da Abas ɗin a Shoprite harma da kiran dayakewa Aimanah bata ɗagawa duk yasani zuba mata idanu kawai yayi yana jiran Abas yakawo kansa, Yaya Mansur ya kalli Anty Ummi yace "Masoyiya inada bako fa mai zaki shirya masa?" "Duk abinda kace Masoyi" "Ok asamar masa abu mai sauki na snack yana hanya, yanzu Mus'af yafaɗamin Abas zai zo" yafaɗa ahankali yana kallon inda Aimanah take itada yara saboda karta ji abinda yafaɗa, "Wai da gaske kai nayi farin ciki muna da babban bako, "Aimanah bar yaran nan da Abbansu mu shiga kicin, koma dai jeki kawai ki shirya, kiyi gayu sosai babban waje zamu" "Allah Anty kice na kure wankana" Aimanah tafaɗa cikeda ɗoki, Anty tawuce kicin tana dariya yayin da Aimanah ta shige ɗakin su Zaheed nan komai nata yake anan ta sauka tunda tazo, gefan gado ta zauna tareda kira a wayarta "Mah bakiyi kewa ta ba?" "Kefa Aimanah kin fiya rigima kewa kuma kamar wata karamar yarinya nan da watani ma aure zan maki ki tafi gidan mijinki " Mah tafaɗi haka tana dariya "Shikenan Mah bazan dawo ba anan zanyita zama tunda bakwa nemana, kuma ni bazanyi aure ba" "Muna nemanki mana amma yaya zamuyi tunda Yayanku ya rike ki, kilama kinzo Abuja kenan, jiyan nan Daddy ke cewa yakamata ki dawo Monday zaku koma school nan da kwana takwas" "Mom nadawo Abuja fa da zama kika ce?" "Au Suɓul da baka ne, inake ina Abuja wannan garin sai su Zaheed" "Mom gobe zan dawo, garin nan ya isheni ba inda nake fita fa daga gida sai gida inkinga mun fita to shoping mukaje" "A'a karki tawo gobe, kijira sai friday muna Kaduna nida Daddynku gidan ba kowa sai Alhamis zamu koma gida" "Mom mai ake a Kaduna?" "Daddy yazo samina shine muka tawo tare" "Wow Mom kuna lokaci fa keda Daddy yanzu nan da Kaduna saida kika biyosa?" "Ki kiyaye ni Baby, kyalesa zanyi yatafi shi kaɗai yammatan zamanin nan su kallemin shi, ina bazanyi wannan saken ba, abaya ba'amin kishiya ba yanzu ba zan bada wannan damar ba" dariya Aimanah tayi tareda kashe wayar tana dariya sosai, yanda Mahh da Daddy suke wani abin kamar sabbin aure😂da sauri tamike ta shige bathroom tana faɗin "Ainamah yi wanka ki shirya kafin Anty Ummi tazo tasaki a gaba tana mita" ilai kuwa tana fitowa daga wanka saiga Anty Ummi ta shigo "Nashiga aljannah ni Sa'adatu daman wai baki gama shiryawa ba to maza ana jiranmu" closet ta buɗe tazarowa Aimanah wata doguwar riga ta atamfa data sha stonework sai walwali take "Saka wannan inkin gama shiryawa ki sameni a falo ina jiraki" Aimanah a nutse tagama shiryawa ta ta feshe jikinta da kalolin turare masu sanyin kamshi ta kafa ɗaurin ɗan kwali kalar na yammatan wannan zamanin sosai tayi kyau, wayarta ta ɗauke ta kashe solpie tana murmushi "Mustapha" tafaɗa a hankali tunawa da tayi ko wanne lokaci in tayi kwalliya irin haka takanyi hoto ta tura masa yayita yabawa. Jiki a sanyaye ta fito falon, Anty Ummi ta tarar tsaye gaban danning tagama haɗa abubuwa saman babban plate, "Kai tawan Masha Allah kyau iya kyau, karɓi wannan kaiwa su Yayanki falon baki, yayi bako leena bata nan taje kasuwa" Aimanah bata kawo komai a ranta ba ta ɗauki plate ɗin ta wuce, bakinta ɗauke da sallama tashiga falon kanta a kasa ta ajje farantin hannunta kan babban teble ɗin dake tsakiyar ɗakin ta juya zata fita ta jiyo muryar Yaya Mansur nacewa "Ke baki iya gaisuwa ba" da sauri ta jiyo ta kalli yayan nata ta tsugunna har kasa tana gaida bakon wanda bata ɗago taga ko waye ba, taji dai muryasa kamar tasan muryar amma bata wani damu dataga wane ba ta fita, taɗan soma tafiya taji muryar Ya Mansur na kiranta ta tsaya cak batare data jiyo ba "Malama koma ciki bakonki ne, ki tsaya ki saurare sa da kyau kiji da abinda yazo, duk da mun riga da mungama magana, shi zaki aura nagaji da wannan halin naki" "Yaya kafa.." "Kimin shiru malama ba kanki fa aka fara soyayya ba'ayi aure ba ni tawa masoyiyar ma mutuwa tayi haka na hakura na auri wata wuce ki shuge ki bani guri kuma kika masa hauka na rugurguzaki wallahi" "Yaya nifa bazan iya..." "Zaki wuce ciki ko saina zaneki" Yaya Mansur yafaɗi haka yana nannaɗe hannun rigarsa, da sauri Aimanah ta shige falon ranta ɓace, Yaya Mansur yayi murmushi yasa kai ya wuce Abas yabi Aimanah da kallo wacce ta zauna saman kujera bata ko ɗago ta kallesa ba "Amincin Allah ya tabbata a gareki tauraruwa ta" kallo ɗaya Aimanah ta masa bata sake kallon saba tayi kasa da kanta tana goge hawaye, har Abas yagama maganganun dazaiyi bata kula saba tana kallo yafice bayan yayi mata sallama, Abas mutum mai naci da kafiya akan abinda yake sone hakan ne yasa bai gajiya ba wajan zuwa gidan yaya Mansur, haka kullum yakan turo mata messages na barka da safiya, haka da dare ma zai mata messages na zafafan kalaman soyayya, tun Aimanah na share sa bata ɗaka kiran wayarsa harta soma ɗaga kiran koda bazata ce masa komai ba, suna a wannan yanayin Aimanah ta koma kano haka yamaida kano wajan zuwansa duk da bashida kowa acan, daga karshe har mahaifiyarsa Hajiya Hafsat saida ya taso Hajiyarsa tazo har gida ranar Allah yasa mutanan gidan suna nan Aimanah bataje school ba haka Mah bata fita aiki ba ranar aikin dare ne da ita, Ainamah na zaune a falo tana kallo jefi jefi tana danna wayarta matar tayi sallama ta shigo, Ainamah ta amsa sallamar cikin girmamawa ta gaida matar kana ta mike ta kira Mah, Mah mace wayayya dason mutane ta gaida matar duk da kuwa bata santa ba, sai bayam sun gaisa ne hajiya Hafsatu ke cewa Mah "Sunana Hafsatu mahaifiyar Abas dake son Aimanah" "Kai madallah sannu da zuwa ya gida ina Abas ɗin ko ya koma Abuja?" "Yan nan yanzuma tare muke dashi ya tisani a gaba da mitar nazo naga Aimanah nace taso shi" Aimanah tayi kasa da kanta tana murmushi jin abinda hajiyar ke cewa, mikewa tayi zata bar wajan Mah tace "Ki shigo dashi" batace komai ba tayi hanyar fita daga falon, ta duba compound na gidan bata ga motarsa ba kamar yanda yasaba shigowa da ita ciki duk sanda yazo, wajan mai gadinsu ta karasa cikin girmamawa ta gaidasa kana tace "Baba matar data shigo yanzu batare suke da wani ba?" "E! tare suke da Abas yana waje can yafaka motarsa bai shigo ba yadai zo nan mun gaisa" buɗe kofa tayi ta fita, Yana tsaye jikin motarsa ya zubowa kofar gidan idanu, tunda ta fito yake kalonta ita ko idanunta a kasa harta karasa inda yake tsaye jikin motar sa nesa dashi kaɗan ta tsaya ahankali kamar batason yin magana tace "Ina yini ya hanya?" ta haɗe kalaman wajan ɗaya batareda ta jira yabata amsa ba, wani daɗi ne yakume zuciyar Abas yau ɗaya Aimanah ta kulasa harta gaida sa tana tambayar sa hanya "Lafiya kalau Hayatie yakike ya school?" "Lafiya! Mah tace kashigo" "To muje" yafaɗi haka yana nuna mata hanya "kayi gaba na bika a baya" "Naki wayon saidai mu jera" murnushi tayi suka jera zuwa ciki. Mas'ud ya gyara zaman sa ya fuskanci Ammi dake cika tana batsewa jin abinda yakawo Mas'ud ɗin wajanta, harya gama maganar dayake bata katse sa ba har saida yakai aya "Mas'ud kafita a idona ina ganin mutumcinka inda nasan abinda yakawo ka kenan da bazan tsaya na saurareka ba" "Ammi dan Allah kiyi hakuri kinga kuwa yanda Mustapha ya koma, ko ke kika gansa zaki tausaya masa, dan Allah ki masa addu'a kirage fushin nan da kike dashi, fushin ki ma kawai zai iya saka sa a wata masifar da tafi wannan, ki masa addu'a na rantse da Allah ko kaffara bazanyi ba Amarya da Sumayya ba haka suka bar Mustapha ba, ni zuwa nayi muyi magana dake musan mai zamuyi akan lamarin Mustapha, wancan satin fa bakiga yanda yazo office ɗina ba a birkice wai Sumayya ta aikesa ya siyo mata abinci, Mustapha fa Mistaphan da yarinyar nan bata ishe sa kallo ba ace itace yanzu ta aike sa siyan abinci ai daga ji Ammi kinsan akwai wata a kasa" "To Mas'ud maizan maku yanzi?" "Yawwa Ammi haka nakeso ki faɗa yanzu dai daga farko yakamata mu fara masa abinda zai karya wanan sihirin da aka masa" "Taya kasan sihiri ne ajikin Mustapha bayan sihiri ma fa harda hali" murmushi Mas'ud yayi kana yace "Ammi ki yarda dani nafi kowa sanin Mustapha nasan halinsa wallahi mace tayi kaɗan ta hana sa zuwa gareki kema kin sani kinsan soyayyar da biyayyar sayake maki, ki duba yanda duk ya birki ce yakoma kamar ba mutum ba, cemin fa yayi yana son ganin ki inya ɗakko hanya zai zo gidan nan gaba ɗaya saiya manta hanya" "Naji Mas'ud zan haɗa masa maganin karya sihiri jibi kazo ka karɓar masa" "Yawwa Malama Ammi" mirmushi kawai Ammi tayi sukayi sallama Mas'ud ya shiga ɗakin Umma sukayi sallama, wajan fitowara daga gidan ne ya haɗu da Murjana zata shigo gidan itama, ko kallon inda take baiyi ba balle ya amsa gaisuwar datayi masa, Murjana tafaɗa ɗakin Amarya bako sallama tafara magana "Mai wannan gayan na gidansu Aimanah yazo yi gidan nan?" "Murjana kenan ni ina zan san maiya zo yi banma san ya zo ba, kin faɗo min ɗaki ba sallama" "Amarya nifa wallahi badan badan ba da sai nace nima a kama min shi ya shigo hannu nayi wuf dashi kawai gayan yana birgeni, harfa gaida sa nayi yaki amsawa" Murjana tafaɗi haka tana zumɓuro baki irin na shagwaɓaɓɓun yara "Murja ba ba irin wannan nakeso ki aura ba mai nasama yaci balle yaba nakasa, kijira akwai tanadin danake maki wanda zakiyi farin ciki da hakan" "A'a nida gaskiyya Amarya banason wani ni Mas'ud nakeso, kuma dole ki san yanda zakiyi na aure shi ko na tone asirin da muka binne a makabarta...✍🏻 07039793439 [2/13, 4:43 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation Shafi na Biyar "Murjana mai nake ji kina faɗa? akul ɗinki wallahi duk randa kikayi wannan gangancin saina matukar saɓa maki sannan kisa a ranki bazaki auri Mas'ud ɗin ba Salim zaki aura ɗan kawata matar minista ana kai ki inda zaki huta kina cusa kanki cikin wahala mai za'ayi da Mas'ud har maye kuda balle romansa" "Amarya salim kuma ni bana son sa bazan aure saba kin san maganar dayake min ne ɗan iska ne fa" "Ke wai Murjana sai yaushe zaki waye? yar soyayyar nan dayake nuna maki ce iskanci? maye a ciki danya rike hannunki ya sumbata ai soyayyace" "Ni! ni!! ni!!! bana sonsa wallahi abani wanda nakeso ko nayi ba dai dai ba" Murjana tafaɗi haka tana buga kafa irin na shagwaɓaɓɓun yara ta wuce ɗakin Amarya tana cigaba da faɗar maganganu, Amarya tabita da idanu harta shige ɗakin, tashi Amarya tayi daga wajan ta danna wayarta tasoma magana kasa kasa. "Boka tsito mai dogon zamani barka da dare" da wata iriyar murya kamar bata mutane ba yasoma magana wacce ke futowa da wani ihu "Barka dai doguwa mai dogon zunubi maike tafe dake a wannan daran?" "Tsito yarinyar nan Murjanatu keson bani matsala a kan yaron nan Mas'ud kadai san maganar" "Mai dogon zunubi ki bar wannan maganar komai namu zai iya lalacewa in muka shiga shirgin yaron nan a tsaye yake kan addu'a da azkhair gashi mayan karatun kur'ani na duba ta ko'ina naga bazamu sami riba akan yaron nan ba, ita kuma Murjana yau zanyi aiki a kanta zata manta da duk wani sirrinki data sani zamu rike zuciyarta sai yanda kikayi da ita, daga karshe gobe kizo anan zaki kwana kin dai san aikin basai na maki bayani ba" Hmmm Amarya taja Numfashi kafin tace "Tsito na gane amma ina cikin jini hakan bazaiyu ba sai nayi tsarki" "Yawwa hakan yayi daman ina neman jinin al'adar mace wadda tai haihuwa biyu bata sake ba zanyiwa wani ɗan majalissa aiki, kizo goben da wurwuri" Jiki a sanyaye ta amsa masa da "To" ta ajje wayarta tana mita "Gaskiyya boka kana takuramin kai kullum cikin jaraba kai aba ba wani girman kirki ba". *MUSTAPHA* A hanakali yake cakalar abincin da sam ba daɗi ci kawai yake saboda yana tsoron masifar Sumayya wacce ke zaune fegansa ita hankali kwance take cin abincin bata da wata damuwa, wayar Mustapha datayi kara ita taja hankalinsu gaba ɗaya, yakai hannu zai ɗauki wayar Sumayya tariga sa ɗauka, "Aboki" Sumayya ta faɗa tana tsare Mustapha da idanuwa, mika masa wayar tayi "gashi wannan sarkin nacin ne Mas'ud ɗaga kiran kuma kasa a hansfree," haka yayi kamar yanda tace ɗin "Barka da dare Amini na fatan ka wuni lafiya yau gaba ɗaya banji kaba" "Aboki abubuwa ba sauki aikin office ya rikeni ban samu shigowa wajan kaba kamar yanda nace, kasan inata shirye shiryan tafiya india cost ɗin nan na wata uku a satin nan nakeson tafiya" "Yayi kyau ashe da ban kira ka ba sai lokacin tafiyar yayi sannan zaka faɗa? ka gayawa Ammi?" kwarewa Mustapha yayi sakamakon Ammi dayaji an ambata gabansa yai wani irin faɗuwa "Wace Ammi?" Mustapha ya ambaci hakan hankalinsa kwance, Mas'ud saurin jingina yayi da fuskar gadonsa take wasu hawaye masu ɗimi suka zubo masa yasoma sharewa kamar bazaice komai ba sai kuma yamagantu "Mustapha Ammi ce baka sani ba? ashe nima baka sanni ba?" "Freind ka yarda dani na rantse ban santa ba nakasa tuna inda nasan sunan a kasan zuciyata inaji kamar na santa" Mas'ud katse kiran yayi ya kifa kansa saman cinyarsa yafashe da kukan tausayin ɗan uwan nasa "Yazama dole a kaina insha Allah saina fito dake daga wannan mummunan duhun daka faɗa" Sumayya daɗi ne ya mamaye zuciyarta jin aikin da boka tsito yayi masu jiya, aiki yayi sun sa yamasu aikin da gaba ɗaya Mustapha zai manta da mahaifiyarsa su mallake dukiyar sa gaba ɗaya itada Amarya, zuciyar ta fal daɗi ta wuce ɗakinta ta kira Amarya tana faɗa mata yanda Mustapha sukayi da Mas'ud, Amarya tayi farin ciki sosai daman ta riga da ta yadda da aikin tsito daga ka faɗa ne bukata zata biya, har rawa rayi tai juyi a cikin ɗakinta, Murjana na mata dariya, tsakar gida ta fito tayi ko sa'a Ammi ta fito daga ɗakin Momy uwar gidansu, Amarya ta fashe da dariyar keta tayi tsalle tai juyi ta fara yar waka "Daka haifi gwammana gwara ka haifi matar gwamna saini Amarya surikar Mustapha yau ya gwangwaje ni da kujerar hajji, ƴa mace kyautar Allah wata ta haifi maza ta haifawa wasu ita da banza ɗaya suke a wajan ɗanta" Ammi murmushi tayi harta soma tafiya zuwa ɗakinta sai kuma ta tsaya ta maida martani dan tasan kai tsaye Amarya da ita take "Amarya ki fita sabgata zan matukar saɓa maki a gidan nan, nafa sani nariga nasan komai aikin asirin, na riga na bar maki shi ke da yarki na godewa Allah dayasa ba shi kaɗai na haifa ba bare abin yadaman" "Saude ni kike gayawa na ma ɗanki asiri inace nan nan yazo har ɗakina yace yanason ƴata Sumayya daman sai da nace masa bazan basaba yanace saboda nasan kun riga kun tsane ni a gidan nan" Amarya tafaɗi tareda fashewa da kuka, Alhaji Kamal da yaji kukan Amarya fitowa yayi daga ɗakinsa "Ya isa nace ya isa wai mayake damun kune da daran nan zaku tayarwa da mutane hankali, ke Saudat na fuskanci tunda akayi auran nan kin tashi hankalinki kin tisa naja'atu a gaba kamar ita tace Mustapha zoka auri yata" Momy tai saurin kallon mijin nasu cikeda mamakin sauyawarsa a jiyan nan mafa sunyi magana akan auran Mustapha da Sumayya har yace yana tausayin Ammi ganin yanda ɗanta ya juya mata baya ko gidan ya shigo shi da Sumayya basa shiga inda Amni take ɗakin Amarya kawai zasu shiga su gama abinda zasuyi har subar gidan baya ko kallon ɗakin Ammi "Alhaji laifin Ammi ka gani ai kuwa idan ba'a tausayawa Ammi ba ba'a ga laifinta ba, inace jiyan nan..." "Ya isheki haka Asiya daman ai na lura kun takurawa Naja a gidan nan da da take faɗar kun haɗe mata kai bana yarda yanzu naga zahiri, ke Amarya shige ɗakinki barni da matan nan zanyi maganinsu a kanki zan iya aika ko wacce gidan su" Momy mamaki yakashe ta ta dafe baki🤔kawai tana kallon Amarya, Ammi batace komai ba ta karasa ɗakinta, Amarya ma komawa ɗakinta tayi tana jinjinawa aikin Boka tsito dan jiyan har Alhaji Kamal tace a haɗa duka a ɗinke bakinsa akan auran nan yadaina ganin laifinta, saura Momy ma zatayi maganinta itama. Ammi zama tayi saman kujera tana goge hawayan dayake fitowa daga idanunta Saheed ɗanta na uku daya ji komai saboda yana falon Ammin yana kallon kwallo, kashe kallon yayi yadawo kusa da mahaifiyarsa yana goge mata hawayan dayake zubowa daga idanunta, tsabar takaici takasa magana wani abu ya tokare mata a kahon zuci, shigowar Ahmad ɗanta na biyu wanda suke matukar kama shida Mustapha ganinsa yasa tafashe da kuka, da sauri ya karaso inda take ya zauna a kasa ya kifa kansa saman kafafunta ji yake kamar shima ya fashe da kukan yanzu Surayya takirasa ta gaya masa abinda Abba yayi a gidan, Shaheed ya ɗora kansa saman kafaɗar Ammi yana tayata kuka, jin kukan da Saheed yake yasa ta katse nata kukan tasoma ajjiyar zuciya a jere a jere, idanunta ta rufe "Shaheed yi shiru daina kukan nan bakai yakamata kayi kuka ba ni ce zanyi kuka an cuce ni, ana kuma ganin laifi na, ni Alhaji ke gayawa magana duk hakurin danayi bai gani ba, gobe zan bar gidan nan ku maza ne ba mata bazan iya zaman hakuri ba, Ahmad kayi aure kabar cikin gidan nan kafin wata masifar ta ritsa da kai zanso ka auri Aimanah hakan zai faranta raina, Shaheed zan tattara kuɗaɗe na nasama maka makaranta a malesia ko thailand katafi can kayi nisa da gidan nan kaima" "Ammi munyi maganar nan dake tun kwanaki bazan iya auran Aimanah ba bazan so abinda ɗan uwa na ke so ba koda Yaya Musty baya raye bazan iya auran Aimanah ba, bare yana raye wani abu ne ya gifta yasa ba'ayi auran suba, har yanzu ina addu'a Allah ya warware kullin da akayi Yah Musty yadawo hankalinsa ayi auransa da Aimanah" "Ammi niki nema min auran Aimanah zan aure ta" Shaheed yafaɗi haka hankalinsa kwance, Ammi da Ahamad tare sukayi dariya kafin Ahamad yace "Ina kaga an taɓa haka Aimanah ta girmeka nesa ba kusa ba kai ba sa'an auranta bane yaushe ka gama scoundry ita ko datake fenal year a jami'a" "Yah Ahamad ai ba haramun bane basai mu tafi malesia tare ba nifa dama can ina yin Yaya Aimanah kawai dai matsalar banida aikinyi" Ammi dariya ta kuma yi tareda shafa kan Shaheed tana murmushi. *Aimanah* Agajiye ta tashi daga barci sauri sauri ta shiga bathroom tayi wanka cream kawai ta murza a jikinta ta fesa turare kan doguwar abayar data saka ta fito, kamar yanda tayi zato hakan ce ta tabbata gaba ɗaya mutanan gidan na bisa danning ana breakfast wajan Daddy ta soma zuwa hannunta tasa ta rungomo Daddy ta baya ta kwantar da kanta saman kafaɗarsa tana kallon fuskarsa tace "Goodmorning Dad" "Morning my lovely Douther ya kike hope kin tashi lafiya" "Lafiya kalau na tashi Dad" wajan Daddy ta bari ta nufi Mahh dake cin abincinta kai bazaka kace tana kallon suba saboda gaba ɗaya hankalinta yana kan abincin datake ci "Kinga basai kin zo ba sarki son jiki ni karki zo ki wani makalƙaleni kamar wata mage, ja kujera kici abinci malama" Aimanah ta ɓata fuska ta tsaya inda take tana kallon Yah Ma'aruf dake mata dariya "Kaga Yaya kadaina min dariya" "Ni kuma Allah ma yasa abinci na nake ci bana kallonki" Ma'aruf yafaɗi haka ganin irin kallon da Mus'af ke aika masa shiyasa yai saurin waskewa, Mus'af mikewa yayi daga kujerar dayake kai yazo inda Aimanah ke tsaye ya haɗa ta da jikinsa kaɗan ya ruko hannunta har gaban teble yaja mata kujera ta zauna ya zuba mata fankaso cikin plate kana ya zuba mata miyar agushi data sha wadataccan naman rago a bowl ya mika mata gabanta "Maza cinye min wannan na ajjeki a makaranta" "Yah wannan fa yamin yawa" tafaɗa ranta ɓace tana cuno baki gaba "Ok karki cinye baki shirya siyan mota a wannan watan ba kenan" da sauri Aimanah tafara cin abincin tana dariya "Na shirya fa yaya Dan Allah camry nakeso" "Bakida damuwa nagama haɗa kuɗina cash Mahh kawai nakeso ta amince banida damuwa da Daddy yardar Mah nasan itace tasa" "Haka mukayi dakai" Daddy yafaɗa yana dariya,Ma'aruf yace "Daddy kowa fa yasani agidan nan Mah itace batason mu huta" dariya a kayi gaba ɗaya banda Mas'ud daya kasa cin abincin gabansa yayi shiru kamar mara lafiya...✍🏻 07039793439 [2/13, 4:43 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation Shafi na Shida Wanan shafin gaba ɗayan sa sadaukarwa ne ga masoyan wannan book ɗin musamman ƴan zauran Mami Yusuf Daboo🥰 Mah ta ajje cokalin hannunta tana kallo Mas'ud da damuwa ta bayyana karara a fuskar sa, sosai tabada hankalinta wajansa, musamman ganin yanda tai magana baiji ba hakan yatashi hankalinta sanin halin Mas'ud mutum ne mai faran faran kusan duk cikin yaran yafisu fara'a da surutu ga kirki da son mutane, ba kasafai ta fiya ganinsa a irin wannan yanayin ba, da Mus'af ne sam batada damuwa dashi saboda shi halinsa ne ciccin magani da miskilancin rashin magana da kin mutane, "Ma'aruf taɓamin na kusa dakai koya kurum ce ne ina magana baiji ba" Ma'aruf yasa hannu yataɓa Mas'ud, Mas'ud jin an taɓa sa yasa ya tsorata yaɗago a firgice, tsam Maah tamike daga inda take ta karasa ta tsaya a kansa cikin kulawa tasoma taɓa jikinsa taji ko zazzaɓi ne ajikinsa tasan rago ne shi, idan zazzaɓi yakamasa baya masa ta daɗi, jikin taji sanyi kalau ba alamar zafi,alamun kalau yake damuwa ce kawai "Sarkin maka lafiyarka kalau kuwa?" "Mah ba kalau ba" Mas'ud yabata amsa batareda yaɗago ya kalleta ba "Taso mu shuga ciki muyi magana" "Maganar bata sirri bace Mah ayita nan kusan ta shafi kowa dake nan akan Mustapha ne?" Mah takoma wajanta ta zauna tana kallon Mas'ud tace "Kai nake sauraro sarkin maka" murmushi yayi ba karamin daɗi yakeji ba idan Mah ta kirasa da sunan nan, "Mah Mustapha na cikin masifa! jiya nakirasa..."kaf ya kwashe yanda sukayi da Mustapha ya gayawa Mah, gaba ɗaya Mah hankalinta yatashi tarinka ambatan "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un yanzu har masaifar takai haka na shiga uku ni Aisha" Mah wayarta ta ɗauka ta wuce ɗakinta, prop bayanta yabi, sam ko kaɗan Alhaji Faruok Mai naira baya kaunar ganin gudaliyar matarsa cikin matsala, Mah wayar Ammi takira Ammi na ganin kiran ta ɗaga da sauri dan tana cikin damuwa takira wayar yayar tata yafi a kirga amma saita jita a kashe "Mah ina cikin masifa abubuwa sun run caɓe yaya zanyi?" "Kiyi hakuri Saudat bansan abin yakai haka ba kwanan nan kinsan haɗuwa tayi mana wuya sanda zaki tashi a aiki ni kuma sannan zan tafi nawa, jiya nake cewa inna koma aikin safe nan gidanki zan wuto inna tashi,yanzu kuma Mas'ud yagayamin abinda yatashi hankalina" "Ki bari Maaa wallahi yaron nan yana cikin jarabawa Allah ya fiddasa daga wannan masifar da haushin sa nakeji yanzu kuwa tausayin sa nake ji" "Ba komai Ammi komai zai wuce yazama tarihi insha Allah yanzu mu haɗu gida anjima zanyiwa su Yaya Muntari magana, mu haɗe gidan Ana zan kira Alhaji usaini ma, sannan karki kuskura ki gayawa Hasana komai kin santa da masifa yanzu ta baro Qatar tazo tayi ta bala'i da mutane" "Bazan gaya mata ba jiyama munyi waya tana tambayata Mustaphan nace mata baya nageria ya koma jordan,wallahi Maaah nakasa aikata komai a makarantar nan jiya na gayawa yara zamuyi test yau amma nakasa shiga class" "Yi hakuri daure kiyi komai yanda kika saba khairan insha Allah" Maah data gama waya ta kalli prop dake zaune gefan gadonta yayi lamo kamar wani karamin yaro "Lafiya na ganka a wannan yanayin prop" "Lafiya kalau kawai banji daɗin labarin nan danaji daga bakin Mas'ud ba," "Mata masifa ne! ni daman tun farko matar nan ta Alhaji Kamal batamin ba kawai dan ya nace ne na gaya masa yaki ji, dayabi tani bazai aure ta ba" "Ya za'ayi prop haka Allah ya tsara matar sace kaga harda ƴa a tsakani ai dole ayi aure, ni da cewa nayi zan aiki Mas'ud wajan yaya liman can kauye koda abinda za'ayiwa Mustapha" "E kiyi hakan jiya ma gwaggo ta kirani bikin jikarta nan da sati biyu" "Allah yakaimu, Aimanah naji tana maganar zuwa kauye sai tayi shirin zuwa biki nikam banajin zanje, satin ne bikin Raudah". Ainamah shirye cikin shirinta na tafiya makaranta tayi sallama a ɗakin Mah ta nemi izinin shiga maa tayi mata izini sannan ta shiga, sallama tayiwa Maaa da Daddy ta fito, ta tarar har Yah Mus'af yafitar da motarsa wajen gidan, a can tasame sa ta shiga yatashi motar suka soma tafiya, Aimanah wayarta take dannawa Yah Mus'af yakira sunanta ganin yanda ya kira sunan nata ya tabbatar mata da magana zai mata mai mahimmanci hakan yasa ta saka wayarta cikin hand bag ɗinta ta ɗago tana kallonsa "Aimanah bani aron hankalinki" sake nutsuwa tayi tana cigaba da kallon sa shi kuma hankalinsa na bisa titi "Aimanah Abas yana matukar sonki, naga ke kuma hankalinki baya kansa, nakasa gane inda kika nufa, inma har yanzu Mustapha ne a ranki to kiyi gaggawar shire sa sabida ko yau Mustapha yadawo hayyacinsa yazo bazan taɓa amincewa da auranku ba saboda wahala zaki sha zama da irin mutane su Amarya ba abu bane mai sauki indai akace maki abu akwai asiri ka nisanci abin nan duk tsananin son da kakewa abin, koda kin auri Mustapha bazasu taɓa bari kiji daɗin gidan auranki ba, haka yasa yanke hukuncin Abas zaki aura, akwai freind ɗina da muke aiki dashi a asibiti shima ya nuna yana sanki na taka masa burki saboda naga shi ɗan tsalle tsalle ne yau kajisa anan gobe acan, kirike Abas sosai yana matuwar sanki zan iya rantse maki da Allah yafi Mustapha sanki, mahaifiyarsa na sonki in har kika aure sa insha Allah bakida matsala a gidansa, sai dai binciken danayi antabbatar min shi ɗin soja ne,zaki iya auran soja?" ya karasa faɗa da murmushi yana kallota "Zan iya auransa tunda har kana sonsa nima zan so sa insha Allah duk abinda kake so nima inaso" "Au zama ki so sa wai har yanzu baki sonsa cab sannunki" "Yah Mus'af duk bazaku gane ba, baku san irin son da zuciyata takewa Mustapha ba, har a ɗazu da safe gani nake kamar ko wanne lokaci zai iya zuwa gareni, amma daga sanda Yah Mas'ud yafaɗi maganar nan nasan Musty yariga da yamin nisa koda ayau zai dawo gareni bazan iya auran saba, inna dawo daga school zan kira Abas zan faɗa masa na amince dashi yaturo iyayansa" "A'a karki saurin cewa yaturo iyayansa ku fara fahimtar juna tukun kisan halinsa yasan naki" "Nariga da na yarda da binciken ka tunda har ka amince dashi nasan halayansa masu kyau ne, bazaka taɓa zaɓan abinda kasan yanada matsala ba" "Hakane my kanwa zan saka maki credit a wayanki ki kirasa, amasa zafafan kalamai wanda zai sa ya manta hanyar kano" Dariya Aimanah tayi saboda tina lokacin da tafara soyayya da Mustapha Yah Mus'af ke faɗa mata zafafan kalaman da take tura masa duk safiya"To naji zan faɗa masa amma ka sake faɗan wasu ba irin na Mustapha ba" "Hhhhhh yarinya nemo da kanki ni zan maki zaman aure ne, nifa zamanki kawai nake a kasar nan daga randa aka ɗaura maki aure zan wuce Rasha na cigaba da karatu" Aimanah hawaye tafara sharewa, dariya yayi mata yana tuna mata randa ya tafi A B U zariya yanda ta rinka kuka shima yana tayata, sunata hira har suka karasa ya ajjeta a B U K shi kuma yadawo zuwa Asibitin Aminu kano inda yake aiki. *ABAS* Kwance yake a ɗaki zuciyarsa fal damuwa gaba ɗaya bayajin daɗin kwanciyar, agogo ya kalla yaga biyar saura minti biyar 04:55 pm dafe kansa yayi dayaji yasara masa, hannunsa na dafe a kansa yamike yanjin jiri kamar zai faɗi, labulan window yaɗaga ya kara gudun A c yakoma gefan gado ya zauna yana tina kalaman mahaifiyarsa "Abas kayi hakuri da yarinyar nan naga kamar ba kaine a agabanta ba kamar tanada wanda takeso a zuciyarta" "Hajiya bafa kowa a zuciyarta yanzu, kawai wani can banza ne yadasa mata tabo a zuciya wanda yasa takejin haushin maza take ganin kamar duk halinmu ɗaya" "Bazadai ka hakura ba kenan?" "Hajiya ayi min addu'a kawai Allah yazaɓa alkhairi" "Amin kagama magana nima inason yarinyar yanayinta yayi min batada hayaniya gata da kunya ba kalar yammatan wannan zamanin bace, duk da na lura gidansu akwai dadtako manyan mutane ne, sun bawa yaransu tarbiya" "Hakane Hajiya nima abinda na gani kenan shiyasa na nace" "Saika cigaba da nacin nidai na baka nan da sati guda indai yarinyar nan bata canza ba ka hakura kawai ga Nafisa nan ƴar kanwata kaje kawai ayi yar gida" shiru yayi bayan ya gama tina maganarsu da hajiyarsa, zafi yakeji sosai duk da sanyin A C daya mamaye ɗakin shi gumi yake haka kurum yakejin faɗuwar gaba yau tinda yatashi aduk sanda yatina da Aimanah sai gabansa ya faɗi, bathroom yashiga yayo wanka yafito ya tsaya gaban madubi yana karewa kansa kallo yana neman abinda ya gaza a jikinsa da har Aimanah ta kasa karɓar sa a matsayim masoyi, ba laifi shi ɗin kyakkyawa ne ajin farko irinsu ne ake kira da black beauty, baki ne shi wankan tarwaɗa inji hausawa bakinsa mai kyau ne, yanada tsayi sosan sosai bashida kiba tsayin sa shiya shanye kibar sa, yanada doguwar fuska mai ɗauke da ɗan madaidaicin bakinsa, idanunsa ba farare bane launinsu ya ɗan sirka da ja, kasancewar yanada matsalan ido, sumar kalar ta filani a kallo daya inka masa zakasan sun haɗa jinsi da filani, shafa kwantancan gashi kansa yayi da yasha gyara, ya busa iska a bakinsa ya furzar da iska mai zafi yana jera ajjiyar zuciya, shiri yayi cikin kakin sojoji yai matukar masa kyau ya saka gilashi a idonsa wanda yake kara masa karfin gani, glass ɗin ba karamin kyau yayi masa ba, ya fito daga ɗakinsa hannunsa na rike da hular sojoji, sojoji ne birjik a compound na gidan nasa sun kusa guda goma, da sauri wani yatawo garesa ganin ya nufi mota ya buɗe masa murfin mota, ya kame waje ɗaya tareda sara masa, Abas yai murmushi yasa kafa ya rofe mirfin motar ya buɗe murfin gaban motar ya shiga frot seat, sojan ya maida murfin motar ya rufe ya zagaya da sauri ya shiga drever seat yatada motan, saida suka hau babban titi kana yace "Oga ina muka nufa?" "Brecck" Abas yabasa amsa batareda ya kalli inda yake ba yaci gaba da magana "Joshua nasha gaya maka ka daina buɗemin bayan mota nafison zama na anan amma bakaji" "Sir wani iri nakeji idan kana kusa da ni ba girmanka bane zama anan kagi dacewa da bayan ni ina nan ina aikina" murmushi Abas yayi yamaida hankalinsa kan wayarsa sau uku yanayi kamar ya kira Aimanah saiya fasa, yanzuma har ya danna call kiran yafara tafiya yai saurin katsewa saboda yanda gabansa yai wani irin faɗuwa, kansa ya kwantar saman seat ya lumshe idanunsa bai buɗe ba har suka karasa bareck, yanajin gaisuwa da sojiji ke masa tun daga bakin get bai iya amsa masu sai dai kawai ya ɗaga kansa, jin an tsaya yasa ya buɗe idanunsa, yana kallo ɗaya daga cikin sojojin dake tsaye a wajan ya buɗe masa murfin mota ya fito, gaba ɗaya sojojin wajan suka kame lokaci ɗaya suka haɗa baki wajan faɗin "Wellcome sir" suma bai iya ce masu komai ba ya ɗaga kai kawai da sarsarfa ya shiga office ɗin Muhd Ahmad Ɗan batta ( *SOYAYYA DA ZUMUNTA*) ya iske yana nan aiki ma yake a laptop ɗinsa, zama yayi a kujera yai shiru yakasa cewa komai, Muhd ya ɗago kai ya kalli Abas, dariya yayi sosai kana ya rufe laptop ɗinsa ya shiga rera waka "So yakama ni, kauna ta shiga ran wani bai shirya ba" "Moh Dan Allah kabari bakasan yanda nakeji ba, zuciyata saura kiris ta buga" Moh dariya yaci gaba dayi sosai kana yace "Mazaje kana bani dariya wai duk sone ya maida ka haka?" "Moh waike mantawa kayi inace nan kazo kasani a gaba har kuka kamin akan Zuhura sai anyi magana kace tausayinta kakeji ashe taka soyayyar ce tazo harda su kuka akan mace ba gwara ni ba" "Kaga mufar maganar naji karka ci gaba da kiramin Zuhra anan yanzu na tafi wajanta na manta dakai anan, wai har yanzu yarinyar nan bata canza ba, nifa kawai gani nake ka hakura da ita" kiran sallah akayi gaba ɗaya suka mike zuwa masallaci, ɗabi'ar su ce komai suke aka kira sallah sukan ajje sa aje ayi sallah in andawo a ɗora. *AIMANA* [2/13, 4:43 PM] +234 904 746 4048: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/GMAOuujeP6dLtFTHo1Edxx 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na Bakwai* Aimanah tana tashi daga makaranta kai tsaye gidan Ana ta wuce, Ana kakarta ce itace wacce ta haifi su Mahh, Ana yaranta biyar uku mata biyu maza Muntari shine babba sai Aisha mah kenan sai Saudat Ammi sai ƴan biyu Anty Hasana wacce ke aure a Qatar sai Alhaji hussain, Ana da mijinta Alhaji Mahmud suma haifaffun garin ɗanbatta ne kauyansu bashida nisa danasu Alhaji farouk mai naira mahaifin Aimanah. Akofar gidan Anan adaidaita sahu ya ajjeta ta basa ɗari biyar bata tsaya jiran yabata canji ba tayi gaba abinta, da sallama ta shiga gidan, Ana ta washe baki tana faɗin "Ga Aimanah ga Aimanah yau agari" Aimanah ta yi murmushi kana ta tsugunna har kasa tana gaida Ana "Nayi fishi Aimanah fisabilillahi kwananki nawa rabonki da gidan nan"Ana tafaɗi haka tana kyauda kai gefe "Ana kiyi hakuri karatu ya rikeni bana samun zuwa ko ina daga gida sai makaranta, yanzuma Mah tace inbiyo tanan intazo saimu wuce tare" "Allah yataimaka Ummu Aimanah, Aisha basu karaso ba ɗazu wannan ɗan yakirani yafaɗan zasu zo gaba ɗaya ko lafiya" Aimana ba tace komai ba tamike ta shige falon Ana "Wash" Aimanah tafaɗa sanda ta zauna a ɗaya daga cikin kujerun dake tsakiyar falon Ana, danna wayarta take jefi jefi suna magana itada Ramla mai aikin Mah wacce ta shigo bayan ta shigo ɗakin ta kawo mata abinci, tana nan zaune har su Mah sukazo kusan tare suka shigo, gaba ɗaya gaidasu tayi tana kallo suka shige can bedroom ɗin Ana, batasan mai suka tattauna ba amma dai tasan koma maine akan Mustapha ne, wanda yanzu takejin matukar tausayin sa, Yau gaba ɗaya ta nemi son Mustapha ta rasa wani tausayinsa takeji, duk cikin sallolinta azahar da la'asar datayi a makaranta gaba ɗaya addu'o'in da tayi rabi Mustapha tayiwa, sosai takejin matukar tausayin halin dayake ciki, haka wani gefe na zuciyanta na matukar tausayawa Abas ganin irin nacin dayake mata, kenan irin yanda takeji a zuciyarta game da Musty haka Abas yakeji akanta, tabbas batayiwa Abas adalci ba yazama dole ta kira yau basai gobe ba ta amince ta soyayyarsa, wayarta ce tayi kara saida gabanta yafaɗi duk a zatonta Abas ne yau gaba ɗaya bai kirata ba tex ɗinma dayake yawan yi mata yau ko ɗaya baiyi mata ba, sanda ta kalli screen na wayar dariya tayi ganin Yah Mus'af ne "Hello yayana" Amainah tafaɗi haka a shagwaɓe bayan ta ɗaga kiran "Ke ina kikaje?"ba karfe huɗu zaku tashi ba yau? yanzu har shida saura minti goma baki dawo gida ba" "Ina gidan Ana fa Mah ce tagayamin na sauka acan inna dawo" Aimanah ta faɗi haka tana turo baki gaba, tanajin sanda ya yi ajjiyar zuciya sannan ya ce "Mai yasa baki gayamin ba kinsa sai zarya nake daga nan zuwa bakin titi" "Yi hakuri Yaya mantawa nayi, yanzuma zamu tawo gida" tafaɗi haka ganin su Mahh sun fito daga ɗakin Ana gaba ɗayansu fuskarsu ba annuri, sosai idanun Ammi sukayi ja alamun taci kuka ta koshi,katse kiran tayi ganin su Ammi sun nufi kofa, gaba ɗaya sukayiwa Ana sallama ko wanne ya shiga motarsa yaja, Aimanah tana tsaye jikin motar Mahh tana kallon inda Mah da Ana suke tsaye da alamar wata maganar suke tattaunawa sun jima suna magana kafin sukayi sallama, suka shiga mota zuwa gida. *Gidan Mustapha* Jiki sanyaye Mustapha yake haɗa kayansu a trolly, yau karfe bakwai nadare jirginsu zai tashi zuwa India shida Sumayya, wacce yanzu take gefansa tana kwance tana aikin nata na danna waya, shi kuma yana haɗa masu kaya nasa da nata,ɗagowa tayi ta kallesa akayi katari da shima ita yake kallo da sauri yai kasa da kansa, hakanan yarasa dalili baya iya haɗa idanu da Sumayya wani tsoronta yakeji sosai, dariya Sumayya tayi sai kuma can tayi shiru tana kallon sama tunani take a zuciyarta, na yazatayi duk ranar da asirin da akayiwa Mustapha ya karye, tasan makomarta saki ne, tunda shidai daman ba sonta yake ba itace ke sonsa har Amarya ta shiga ta fita ta samo kansa akayi aure, a baya Mustapha ko kallo bata ishesa ba, ta tina zuwanta na farko garin kano wajan mahaifiyarta. Sumayya Habibu haifaffiyar garin katsina ce, itace ƴa ɗaya tilo wajan mahaifinta Malam Habibu, Naja mahaifiyar Sumayya ta auri Habibu tun auren saurayi da budurwa suna matukar son juna Malam Habib alkacin da sukayi aure ɗan kasuwa ne a jahar Katsina lokacin kasuwa na damawa da shi yanada arzikinsa, Amarya na nuna masa so da kauna sosai musamman daya sakar mata tana wadaka da kuɗi son ranta daga ita sai ƴarta ba ruwanra da dangin miji na kusa dana nesa, lokaci ɗaya Malam Habibu ya samu karayar arziki sakamakon kayansa da costom suka kama, aka shiga aka fita amma basu saki kayan ba, rayuwa ta soma canzawa a gidan Malam Habibu, kullum Amarya tana cikin mita da tsangwamar Habibu daga karshe ma tace bazata iya zaman talauci ba ya saketa tayi gaba tasami mai kuɗi ta aura, badan yaso ba dole yasaki Naja duk da tsannin son dayake mata, lokacin Sumayya na ajin farko na sakandire, suka dawo gidan iyayan Amarya waɗanda suma ba karfin ne dasu ba, rayuwarta take son ranta abinda taga dama take ba wanda ya isa yai mata magana Amarya tariga ta raina iyayanta bata wani ɗaukar maganarsu, shekara ɗaya da rabuwa da Habibu ta haɗu da Alhaji Kamal ba ɓata lokaci akayi bikinsu, daga farko Sumayya a wajan iyayan Amarya take zaune harta kammala scoundry, daga baya ta dawo wajan Amarya taci gaba da karatu, bata wani maida hankali akan karatun ba hakan yasa take yawan maimaita aji, daga karshe ma ta watsar da karatun, wata rana tana tsaka da shara a gidan taji gida ya karaɗe da ihun murnar dawowar Babban ɗan Alhaji Kamal Mustapha wanda kallo ɗaya datayi masa ta kamu da so ajje tsintsiyar hannunta tayi tanabin Mustapha da kallo ganin yanda yake rungume kannansa maza da mata har Murjana ya haɗa duka ya rungume, sosai yamasu tsaraba ko alawa bai bawa Sumayya ba wacce ko kallo bata ishesa ba, baya kasar lokacin da Abbansa ya auri Amarya ama yanada labarinta da irin rashin mutumcin datake zubawa duka Anty Halima na gaya masa komai Halima itace babbar yayarsu ɗiya ga Momy uwar gidan Alhaji kamal, shiyasa baya shiga sabgar Amarya yanadai gaidata duk safiya, yauma kamar kullum bayan ya gama gaida Ammi ya shiga ya gaida Momy sannan ya shiga ɗakin Amarya, daga tsaye a bakin kofa kamar yanda yasaba ya tsaya yana gaida ta, ko kaɗan bata wani sakar masa fuska hakan yasa yana gama gaidata yasaki labulan ɗakin yayi gaba zuwa ɗakin Alhaji Kamal, a can ɗakin Amarya bayan sakin labulan Mustapha, Sumayya ta kalli mahaifiyarya tayi kasa da ki ta ce "Mama gayan nan yana burgeni, amma shi na lura bana gabansa ko gaidasa fa nayi da kyar yake amsawa" "Hmm" Amarya taja ajjiyar zuciya kana ta ce "Sumayya nima nayi maki sha'awar auran Mustapha, inada buruka akansa saidai ke gani nake kamar bazaki iya aikin ba" "Mama Allah inason sa kuma zan iya yin komai indai zan auri Mustapha" Sumayya ta faɗi haka tana haɗa hannayanta alamar roko👏daga lokacin Amarya tafara masu garin maganin data ɗakko daga jaka "yace dole sai an zubawa Mustapha wannan a ruwa ko lemu yasha" "Mama wannan ba wani abin damuwa bane, wani sa'in yana bani indafa masa indomie zan haɗa masa da lemu" "Yawwa ƴar gari ina yinki Murja kanki yana ja" a ranar kuwa saiga Mustapha ya shigo gidan yana matukar jin yunwa ɗakin Momy ya shiga yana neman Surayya ta dafa masa Indimie lokacin Sumayya bata nan taje gidan Anty Halima, ɗakin Amarya ya shiga ya kira murjana yace ta dafa masa indomie ta kawo masa ɗakinsa, Sumayya ce ta tayata suka dafa Indomie ɗin harda lemun Genger daya sha garin magani takai masa har ɗaki godiya yayi mata sosai sanda ta nuna masa lemun Genger tana gaya masa ita ta haɗa masa, daga lokacin daya sha lemun nan gaba ɗaya ya birkice kan Sumayya har takai anyi auransu, daga nan suka ɗora da masa banke bankan maganin asiri a abincinsa da abun shansa. Sumayya taja ajjiyar zuciya hakanan taji jikinta yayi mugun sanyi, batasan ma Mustapha yafita daga ɗakin ba saida taga yadawo ɗakin da jaka a hannunsa yana kallon time shida saura minti huɗu "Sumayya taso mu tafi ga Mas'ud can yazo shi zai kaimu airport" batace masa komai ba ta zari mayafinta tabi bayansa, kofar motar yabuɗe mata ta shiga shi kuma ya shiga gaba, Mas'ud yaja motar mai gadi ya buɗe masu get suka fita, har sun ɗan gota gidan Ammi Mas'ud yaja yai parking yana kallon Mustapha "Kayiwa Ammi sallama kuwa"? kai kurum Mustapha yaɗaga alamar A'a, Mas'ud yafita daga motar ya zagayo ya buɗewa Mustapha murfin mota yaja hannunsa ya fito da shi, Mas'ud ya kalli Sumayya ya ce "Sorry Madam bari Musty yayiwa Ammi sallama bazai bar kasar nan ba basa albarkar Ammi" bai jira amsarta ba yaja hannun Musty suka shige gidan, Ammi tana karatun kur'ani taga shigowar su Mas'ud kallo ɗaya tayiwa Mustapha ta ɗauke kanta a gabanta suka tsugunna Mas'ud ya ce "Ammi ga Mustapha na kawo maki kisa masa albarka zai tafi india" "To Mustapha Allah yataimaka ya tsare hanya yabada abinda akaje nema" "Ameen" Mas'ud yace yana kallon Mustapha da yayi shiru yakasa cewa komai yama lura jikinsa sai karkarwa yake, hannunsa yaja zasu fita har sunje bakin kofa Mustapha ya cire hannunsa daga na Mas'ud yadawo wajan Ammi rungumeta yayi na ƴan sakonni kana ya sumbaci kuncinta baice komai ba yafita, Ammi ta shafi wajan da Mustapha ya sumbata tana murmushi ta sumbaci hannun data shafi wajan "Allah ya kuɓuto min dakai Musty" tafaɗa tana share hawayan dasuka zubo mata, Mas'ud suna zaune a recepsion jefi jefi suna ɗan taɓa hira da Musty har sanda aka fara kiran mutane su shiga jirgi, Mustapha ya rungume Mas'ud hawaye na zuba daga idanunsa "Aboki zan tafi kamin addu'a ko yaushe ina jin kirjina yanamin zafi kamar ana huramin wuta a ciki" "Kana cikin addu'o'ina Musty Allah ya tsare kamaida hankali kan cost ɗin nan kasan ka kammala shi zaka sami karin girma a bank ɗinku kilama a canza maka wajan aiki ga wannan" Mas'ud yafaɗa yana mika masa littafin Hislum muslim "Kayawaita karantawa a ko yaushe musamman zikirin safiya da maraice" "Insha Allah" Mustapha yafaɗa bayan ya karɓi littafin, Mas'ud yana tsaye bai bar wajan ba saida yaga tashin jirginsu. Aimanah wanka ta ɗauro alwala bayan ta shirya cikin doguwar rigar barci ta zura babban hijab ɗinta na sallah ta kabbara sallah, raka'a biyu tayi ta idar ta fara addu'ar istikara, ta gama tsab ta ɗora da wasu addu'o'in ta gama ta kwanta a gado, agogo ta kallah taga karfe 10:45pm murmushi tayi ta kira lambar Abas, bugun farko ya amsa kiran kamar daman zaman jiran kiran yake "Nayi fushi masoyi shine yau gaba ɗaya baka kirani ba ba tex ɗin daka saba yimin" "Allahu akubar!" Abas yafaɗa yana tsalle shi ɗaya a ɗaki "Sake faɗa Hayatie da gaske kike dan Allah daga bakinki wannan maganar ta futo?" "Daga bakina ta fito ba wasa, Kalbie nariga da amince da soyayyarka tun safe nake jira ka kirani nayi maka wannan albishir ɗin sai kuma kaki kira" Aimanah tafaɗi haka tana turo baki gaba kamar tana gabansa "Oh Sorry hayatie Moh ne ya hanani kira wai nabari ki kirani da kanki" "Au ai ban sani ba da nima bazan kira ba saina ja ajina" tana gama faɗar haka bata jira yayi magana ba ta katse kiran, tana kallon kiransa taki ɗagawa addu'ar kwanciya barci tayi ta juyawa wayarta baya wacce tana jin kira nata shigowa daga wannan ya katse wancan yashigo....✍🏻 07039793439 [2/13, 4:44 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na Takwas* Abas ya kasa zaune ya kasa tsaye ganin abin yake kamar a mafarki,daina kiranta yayi ganin taki ɗaga kiran ya kira Joshua cikin barci Joshua yaɗaga kiran Abas bai saurari abinda Joshua ke cewa ba ya ce "Zan sami jirgin da zai tashi zuwa kano yanzu?" "Sir kano yanzu? dare yayi ba jirgin zuwa kano yanzu sai bakwai na safe" "Asaimin tiket shida kazo ka kaini airport" "Ok Sir" messages ne yashigo wayarsa hannunsa na rawa ya buɗe tex ɗin _Kalbie ka kwanta kayi barcin, bazan ɗaga kiranka ba sai safiya, fi Amanillah_ yaji daɗin tex ɗin nan sosai ya karanta sa ba adadi kwanciya yayi kan gadon kafafunsa a kasa, Idanunsa na kallon P o p ɗin ɗakin, ya lankwasa hannayansa ya ɗora kansa akai, wani irin bugawa Numfashinsa keyi, da sauri ya ɗauki wayarsa ya dannawa Hajiyarsa kira, Hajiya wacce ke kwance jikin mijinta gabanta har faɗuwa yayi jin ring na waya ahankali ta mike zata bar jikin mujinta, hannu yasa yadawo da ita jikinsa ya rungumeta yasa ɗaya hannun ya ɗakko mata wayar, "Abas" Hajiya tafaɗa hankalinta tashe ta ɗaga wayar "Hajiya Aimanah ta amince dani yanzun nan ta kirani" "Abas shine zaka kirani da daran nan da nayi barci fa" "Hajiya bani da wanda zan raba farin cikin nan da shi kin sani sai ke, da inada kanwa ko kani tabbas su zan kira a daran nan" tausayin Abas ya rufe ta ta kakalo murmushi tareda kokarin ɓoye halinda take ciki ta ce "Nayi farin ciki Abas Allah yasa albarka ka turomin lambar ta zan kirata da safe, amma kadaina kirana a irin wannan lokacin kasan dai lokacin Abbanka ne" dariya Abas yayi ya katse kiran, tareda sake kiran lambar Aimanah, Aimanah wacce barci ya fara ɗaukarta firgigit ta farka jin karar wayarta "Wo Abas" Aimanah ta faɗa tana lumshe idanu, ta maida kanta ta kwanta karar shigowar tex bayan kiran ya katse yasa ta ɗauki wayar tasan ba tantama Abas ne _Hayatie ki ɗagamin kira inaso naji muryarki nayi barci mai daɗi Inba haka ba zan tawo kano yanzu_ "Hmmm Abas" tafaɗa ta kashe wayar gaba ɗaya ta maida kanta ta kwanta. Ammi cikin barci taji wayarta na kara alamar kira, buɗe idanunta tayi ta janyo wayar bata tsaya duba ko waye ba ta ɗaga kiran "Ammi barci kike ki tashi mu raya daran nan kinsan matsalar da muke ciki" "To Mah nagode" Mah bata sake magana ba ta ajje wayar kan daddumar data ke kai taci gaba da jan carbinta Istingifari tayi guda ɗari ra ɗora da salatin annabi kana ta fara jero addu'a wacce gaba ɗaya kan Mustapha Allah ya fitar dashi daga halin dayake ciki, acan gidan Ammi ma alwalan tayi ta tada salllah haka mahaifiyarsu Ana itama sosai ta raya daran da sallah haɗeda addu'o'i, Aimanah washe gari bayan tayi sallar asuba barci ta koma bata tashi ba sai bakwai da rabi, cikin mintuna da basufi talatin ba tayi wanka, yau kasancewar garin antashi da sanyi yasa ta sanya riga ja da bakin wando ta ɗora doguwar rigar sanyi wacce tazo mata har gwiwarta tasa hula da karamin hijab daya sakko ya rufe kirjinta, da sauri ta fito ganin har takwas ta gota al'adar gidance karfe takwas ake zaman breakfast, kamar jiya yau ma kowa ya rigata zuwa wajan banda Daddy da jiya ya tafi legos sai Mah da taga bata fito ba, gaba ɗaya tayi masu jam'i da ina kwananku, tare suka amsa tamaida hankali wajan cin abincin saboda yau da yunwa ta tashi, Yah Mus'af na lura da ita na yanda yau ta zage tana cin abinci sosai abinda suka daɗe basu gani ba tun sanda ta shiga kuncin rabuwa da Mustapha, wayarta ta kunna kamar jira ake kira ya shigo, dafe kai tayi ganin Abas ne mai kiran, kamar bazata ɗaga ba sai kuma ta ɗaga batace komai ba "Barka da safiya abincin ruhi na" "Hmmm Barka dai! ya kake" Aimanah mikewa tayi zata bar wajan ganin gaba ɗaya yayun nata sun zuba mata idanu suna kallonta musamman ma Mas'ud wanda yakasa jurewa sai da yabiyo ta har ɗakinta lokacin ta gama wayada Abas "Ke dawa kike waya?" Mas'ud ya watso mata tambaya yana tsareta da idanu "Uhmmm ummm Abas ne" "Waye Abas?"koma wane ki gaya masa an maki miji" da sauri ta ɗago ta kallesa batace komai ba saboda maganar Mus'af da taji daga bayan yaya Mas'ud wanda bata sanma yana ɗakin ba, yana tsaye jikin kofa ya ɗora hannunsa ɗaya saman kofa ɗayan kuma ya rike kugunsa dashi "Yah Mas'ud waye yayi mata miji?" "Kai mai kake anan?" "Yaya ba wannan ba tambayya nayi" "Ni nayi mata" Mas'ud yafaɗa a zafafe, Mus'af yayi dariya har ya juya zai fita daga ɗakin sai kuma ya dawo yana kallon Mas'ud ya ce "Yaya nasani kana taya abokinka kishi ne, amma kasani yanzu ba Mustapha a zuciyar Aimanah, haka ba wanda zai mata dole anan dan haka ka zuba idanu kawai Aimanah ta sami mijin aure wanda yafi Mustapha" Mus'af yana gama faɗa yasa kai ya fice daga ɗakin Mas'ud yabi bayansa a zafafe, hayaniya suka fara yi wanda yasa Mahh ta fito daga ɗakinta tana kallonsu "Yau kuma yarinta za'amin a gidan nan" Mah tafaɗa tana kallon yaran nata da basu san ta fito ba daga ɗakinta, "Mah ni yaron nan zai tsaya yana gayawa magana, na lura yaron nan shiyake so ya cusawa Aimanah soyayyar wani ba Mustapha" "To Mas'ud ina Mustaphan yake yanzu zama zamuyi tayi da ita muna kallonta har Mustapha yadawo, ba wannan maganar kabar Aimanah ta so wanda zuciyarya ke so, koda Aimanah har yanzu Mustapha take so bazan yadda ba na kaita gidansa wanda bazata tsinci komai ba a gidan sai tarin wahala kishi da Sumayya ka zaɓa mata, kana kallon halin da ake ciki amma kake kokarin kare soyayyar Mustapha karna sake jin hayaniya a tsakaninku kan wannan maganar, kai Mus'af bawa Mas'ud hakuri kuma karna sake jin sa'insa a tsakaninku koba akan wannan maganar ba" Mus'af yabawa Mas'ud hakuri yai gaba abinsa "Kayi hakuri bawai na goyi bayan Mus'af bane kasan dalili na" "Na fahimta" Mas'ud yafaɗa yana mai wucewa ɓangaran su ransa ba daɗi tabbas da yana da dama saiya ɗaurawa Mustapha aure da Aimanah saboda yasan duk randa Musty yadawo Mustaphansa akwai matsala in Aimanah taƙi sa, Mah ta kalli Mus'af daya koma wajan daya tashi yaci gaba da cin abincin sa "Karage zafin zuciyar nan taka Mus'af" "Insha Allah zan rage" Mus'af yafaɗi haka yana cigaba da cin abincinsa, "Gobe ka shirya zaka kaini Ɗanbatta" "Mah inada tiyata fa" "Kullum tiyanta bata tashi sai anyi maganar zuwa ƙauye, Mus'af bafa a raina asali" "Mah bana gudun ƙauye kawai banaso ne naje ayita kallona kamar sunga sabuwar halitta" Ma'aruf yayi dariya sosai wacce tasa har Mah dake tsaye saida ta dara ya ce "Mah Yaya fa bazai kaiki ba kibari ni zan kaiki gobe sunday bazan shiga kasuwa ba, inama Gwaggo Rakiyya zata birgeni data haɗa auranka da Ummita" "Allah ya isa tsakani na dakai" Mus'af yafaɗa tareda ture plate ɗin abincin dake gabansa, Mah dariya take sosai, yanda Mus'af yawani zazzaro idanu shi yafi bata dariya "Ai kuwa ka kawo shawara haka za'ayi bari Daddy yadawo" Mus'af cak ya tsaya daga tafiyar daya fara yi zai bar wajan Mahh dan Allah kar muyi haka dake karma maganar nan taje wajan Daddy shifa ɗaukar maganar zaiyi da gaske ina ni ina wata Ummita mai zanyi da kazamar yarinyar nan" "Kai dai kake mata kallon kazama" Ma'aruf yafaɗa yana cigaba da dariya "A'a Yah Ma'aruf kodai kodai" "Kodai mai karma ki karasa bar maganarki anan kafin na faɗo maki sunan naki masoyin Amadu" Aimanah dariya tayi sosai kamar zata faɗo kasa daga saman kujera "Kasan Allah banakin Yaya Amadu kawai banason kaunar sa ne da ace ina kaunarsa zan iya auransa maye a cikin zaman kauyan wani bin fa sun fimu kwanciyar hankali, kuma ma ai birninka aljihunka" Mah bata sake ce masu komai ba taci gaba da dariyar Mus'af wanda tini yabar wajan,wayar Aimanah ce tayi kara ta kalli screen na wayar tana murmushi ganin Abas ne. Akwana atashi yau Aimanah da Abas sun kwashe watanni tare da Abas soyayya suke sosai kamat baza'a mutu ba😂kusan ko yaushe suna jone a waya duk karshan sati yana kano, tun Hajiyarsa na mita harta zuba masa idanu, Yauma kamar ko yaushe suna tare ta masa rakiya zai wuce Jigawa, Aimana ta gyara tsawarta jikin motar Abas tana kallon yanda yake tsara mata kalamai wanda take jinsu kamar a film, ba shine saurayinta na farko ba amma yanzu kam zata iya cewa ba kowa a zuciyarta samada Abbas, lumshe idanu tayi tareda buɗe su akan kyakyawar fuskar Abbas wanda yai kuri yana kallonta, "Abbas ina sonka sosai, zuciyata bugawa take akowanne bugu tana bugawa ne tareda kaunarka , Abas naroke ka karka yaudare kar..." Saurin katseta Abbas yayi tahanyar faɗin "Aimanah ki manta da wata yaudara banzo nan danna yaudareki ba naroke ki kimanta da *Mustapha* da yaudarar dayai maki ki ɗauki abin a matsayin kaddara da kuma dama can ba rabon aure a tsakaninku, bantaɓa soyayya ba sai akanki kece first love ɗina, uwar ya'yana insha Allah murmusa mana uhmm" Dariya Aimanah tayi tareda saka hannu tarufe fuskarta tana dariya sosai, Abbas ya kalli agogon dake sanye a tsintsiyar hannunsa yaɗago yana kallon Aimana wacce yanayin fuskarta ya canza, idanunwansa yabuɗe sosai yana kallonta tareda ɗaga gira "Aimanah tafiya zanyi kinsan yau zan koma koma Abuja bana son tafiyar dare Hajiya faɗa takeyi, kwara na tafi da wuri, nabaki amanar zuciyarki, ki kularmin da kanki please" "Kema haka My Abas ka kularmin da kanka ka tsare idanunka, karka kalli ko wacce mace" "Kallo?" kallofa love ai daga kanki nagama kallon wata ɗiya mace kema kin sani nafaɗa maki ba sau ɗaya ba biyu ba" sallama sukayi Aimanah ta wuce cikin gida shi kuma yahau motarsa yatafi, ahankali yake tuki cikin zallar nishaɗi shi kansa yakasa gane shin wanne irin so yakewa Aimanah wani iri yakeji idan yana tareda ita jinsa yake kamar nan duniya babu kowa su kaɗai suka rage lumshe idanu yayi yana murmushi tareda tuna ranar farko daya fara gani Aimanah, da wani yammaci da bazai taɓa mantawa ba. MUSTAPHA Wata iriyar rayuwa yake shi ɗaya a india ko kaɗan yaki sabawa da mutane ko yaushe yana gidansa idan ba makaranta ya shiga ba to zaka gansa manne da Sumayya wacce akoda yaushe sonta karuwa yake a zyciyarsa da wani irin matsanancin tsoronta dayake ji Yauma kamar kullum dawowarsa kenan daga makaranta yana shigowa gidan yaji kansa ya sara masa, saurin zama yayi a kasa yanajin ɗakin na juya masa....✍🏻 [2/13, 4:44 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na Tara* *Assalamu alaikum masoya barkanmu da safiyar Juma'a, rana mai daraja idin musulmi, kar amanta dayiwa Annabimu salati a wannan rana haka ma kar a manta da karatun suratul khafi* .......Abas agajiye ya sauka a gidansu can jigawa, bai sami Hajiya a gida ba bata nan taje wajan walimar bikin yar kawarta, bazai iya zuwa ya wuce batare daya ga Hajiyansa ba hakan yasa dole ya kwana a can ba damar komawa Abuja a ranar dole sai washe gari, baisami zama da Hajiya ba sai bayan sallar insha a gaba yasata da hirar Aimanah "Abas ka zurfafa a soyayyar nan fa, ina jiye maka tsoron kazo baka aureta ba" "Hajiya kima daina faɗar haka dan Allah, daman ɗazu wanta yake cemin yakamata na turo manya a tsaida ranar biki" "Hmm jiya muka gama maganar nan da Alhaji, harma yabawa Alhaji Baita dama shida Alhaji Habu yaje suyi komai tunda baya nan" "Masha Allah Hajiya naji daɗi sai dai banso a saka lokaci mai yawa ni zanso ma asa wata guda, daman karatu ya hana komai kinga kuma yau kwana uku kenan da sukayi gradution" "Duk bazai gagara ba daga garemu ba wata matsala sai daga su bansan ko sun shirya ba" "Hajiya sun shirya nifa banason sumin komai zanyi komai da kaina ko ɓangaran Amarya ma Aimanah kurum nakeso kuma ita kaɗai nakeso su kawomin batare da komai ba, ni zan sai komai na gida" "Hakan yayi Allah yasa yanda kake kaunar yarinyar nan kaima tana sonka haka" dariya kawai Abas yayi yana shafar sumar kansa,sallama yayiwa hajiyar ya wuce ɗakinsa yai shirin kwanciya. *Mas'ud* .......Gaba ɗaya bayajin daɗin komai wani iri yakeji idan yaga Abas yazo wajan Aimanah ji yake kamar ya kore sa, haka kurum baisan Aimanah ta auri wani ba Mustapha ba, gaba ɗaya ya hana kansa barcin dare raya darare yake yana addu'ar Allah ya dawo da Mustapha hayyacinsa, yau bayan an fito daga masallaci sallar asuba yabi bayan limamin unguwarsu yayi masa bayanin halin da Mustapha ke ciki, Liman yayi jim kana ya ce "Masa'udu shi wani bin asiri idan anyi wasu binne binne baya sakin mutum har sai anje an tone abubuwan da aka binne, irinshi ne mai wuyar karyewa gashi kace Mustaphan baya kasar nan da sai a haɗa masa ruwan addu'a yasha mugani" "Limana bazaiyu a haɗa ba saina kai masa can kasar dayake" Liman yadafa kafaɗar Mas'ud ya ce "Kayi hakuri kaji kaci gaba da addu'a muma zamu tayaka, idan yadawo kazo ka gayamin akwai abinda zanyi" Mas'ud yayiwa Liman godiya ya wuce gida yanajin zuciyarsa ba daɗi, yinin ranar haka yayi sa gashi nan shiba mai lafiya ba shiba mara lafiya ba, har aka tashi daga wajan aikinsu sanyi kalau da shi, ahanyarsa ta komawa gida kawai yasami kansa da canza hanya zuwa gidansu Mustapha bai shiga gidan ba yafaka motarsa a kofar gidan ya kira wayar Surayya kanwar Mustapha karamar ƴar Momy, yarinyar slantyly yana hango tahowarta ta gilashin motar sa, yanayin yanda take tafiya a nutse yaji wani abu ya daki zuciyarsa murmushi yayi tareda dukan sitiyarin motar, hannu yasa ya buɗe mata murfin motar, bata shiga ba ta ɗan durkusa cikin sanyin murya ta ce "Yayanmu ina yini" haka take gayawa Mustapha shima Mas'ud sau tari hakan take kiransa, "Lafiya kalau Sury, shigo magana zamuyi" "Yaya dadai ka fito Ammi ta hanani shiga mota fa" "Motar samarinki ba, niba saurayinki bane dan Haka ba zance nazo ba" dariya tayi ta shiga motar ta rufe fuskar ta "Yayanmu ka bani kunya ina naga saurayi ni" "To bani kunyar tawa na tafi da ita"dariya ta kuma yi tana sake saka hannunta daya sha jan lalle ta rufe fuskarta "Sury kinsan halin da Musty ke ciki inata ƙoƙarin ganin na fitar dashi amma nakasa yau wani malami yafaɗamin abun da zuciyata takasa nutsuwa" nan yagaya mata yanda sukayi da liman, shiru Sury tayi tana goge hawayan dake zubowa daga idanta "Nifa ba kuka na kiraki kimin ba" Mas'ud yafaɗa da wata murya da ban wacce shi kansa baisan yanada ita ba😂 "Yayanmu dole nayi kuka, jiya nan fa na shige ta kofar ɗakin Amarya naji tana wayada Murjana tana gaya mata ta binne layar nan a kasan murhun mai kosai, kawai jikina yabani kan Yaya ne zasu binne layar" Sury tasake fashewa da kuka "Sury please stop craying, zakisa zuciyata ta buga fa" da sauri ta ɗago ta kallesa, yai saurin basarwa ya ce "Yanzu Amarya tana nan?" "Bata nan ta fita tun safe sai Murjana" "Yawwa kiramin Murjana nan amshi wannan ki goge face ɗinki, duk kin ɓata kwalliyarki da hawaye sai saurayinki yazo yaga fuskarki a haka yamaki dariya" "Yaya Nifa Allah vana da saurayi" "Najib fa?" Saurin amsar hankacif ɗin tayi ta fita tana dariya, yaɗan jima a motar kamar yatafi jin shiru Murjana vata zo ba, yana kokarin tada motarsa ya hangonta ta fito ko mayafi bata saka ba yana hannunta ta rikesa, kai tsaye ta buɗe motar ta shigo bako gaisuwa ta ce "Surayya tace kana kirana" "E! dan Allah mai kike so namaki nima inada abinda nakeso kimin" shiru Murjana tayi alamar tana nunani can taɗago ta kallesa "Kafara faɗar abinda kakeso na maka saina faɗi nawa daga baya sabida nawa yanada girman daba lalle ka iyasa ba" "Nima nawa babba ne" "Zan maka komai kake so matukar zaka aure ni" dam gaban Mas'ud yafaɗi yaɗago ya kalleta ta kashe masa ido ɗaya "Naji zan aure ki indai zaki min abinda nakeso" "Faɗi kawai ko menene zanyi" "So nake ki rakani inda kuka binne asirin da kuka yiwa Mustapha" "Waye yafaɗa maka wannan maganar?" "Narida nasan komai wallahi indai aka tone tona rantse maki zan aure ki" Shiru tayi na mintina can ta ce "Zan tone komai yau da daddare kasani inka yaudare ni komai zai iya faruwa" "Ba abinda zai faru sai alkhairin aure na dake" fita tayi a motar ta koma cikin gida yana kallo harta shiga gidan yatashi motarsa yanajin nutsuwa a zuciyarsa, Surayya tana gayawa Murjana Mas'ud na kuranta ta wuce ɗakin Ammi, ƴar ɗakin Ammi ce sosai kusan komai nata yana ɗakin Ammi, zama tayi saman kujera rufe idonta ta ɗora Hankacif ɗin da Mas'ud yabata a fuskarta tana shakar daddaɗan kamshin turaran Mas'ud, wani bakon yanayi takeji a zuciyarta gameda Mas'ud Mas'ud koda dare yayi kasa nutsuwa yayi har saida yakira lambar Surayya wacce har varci yafara ɗaukarta cikin mayan barcin tai picking call ɗin "Hello" tafaɗa da muryar barci "Haɗani da Murjana ko ki bani lambarta" "Bani da lambarta, naga fitarta ɗazu wajan tara na dare" "Ok" kawai yace ya kashe wayar, Ammi dake zaune kusada Surayya ta kalli Surayya ta ce "Dawa kike waya?" "Yaya Mas'ud ne Murjana ya ke tambayya" Ammi dafe kirji rayi tareda zaro idanu "Wayyo ni Saudatu shikenan shima ya shiga komar su wayyo Allah na" "Ammi vana tunanin wani abu tsakanin Murjana da Mas'ud akwai dai abinda yakawo sa wajanta inaga akan Yayanmu ne" Ammi ta sauke numfashi ta maida kanta ta kwantar jikin filo,Murjana dare tabi ta tone komai batareda Amarya tasani ba saida ta haɗa dukkan abubuwan da suka binne ta kira Mas'ud, yazo ya karɓa cikin dare ya kone gaba ɗaya layun. Alhaji Habu da abokinsa sukaje suka zo kano aka tsaida auran Abas da Aimanah nan da wata uku... [2/13, 4:44 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na Goma* *Wannan page ɗin gaba ɗayansa sadaukarwa ne ga Chamsiyya Louwali Rabo (Mrs Sadauki) Mafiya* *Mustapha* .....Idanunsa yabuɗe waɗanda yaji sunyi masa wani irin nauyi zabura yayi ya fisge kanula ɗin karin ruwan dake hannunsa yamike yana kiran "Aimanah! Aimah!!!" yafaɗa da wani irin sauti da yai amsa kuwa a cikin asibitin, nan da nan likitoci sukayo kansa, wani jirin ne yasake ɗibansa yai luu zai faɗi kafin ya kai kasa ɗaya daga cikin Nurse ɗin dake ɗakin yai saurin tare sa yafaɗi a jikinsa Sumayya gefe ta koma ta ɗora hannu aka ta fashe da kuka ta fita waje ta kira Amarya a waya "Wayyo Amarya na shiga uku shi kenan na kaɗai komai ya warware muna asibiti Mustapha ya birkice sai faman kiran sunan Aimanah yake, Mama dan Allah ki koma wajan boka tsito komai fa ya ruguje" "Sumayya garin yaya kikayi wannan gangancin?" "Mama banida masaniya akan komai kawaifa yadawo gida yafaɗi na kira asibiti suka zo suka ɗaukemu yanzu kuma ya farka yana kiran sunanta" "Bari na shirya naje wajan Tsito muji wannan masifa daga ina da rana tsakan nan" Sumayya ta koma ɗakin da Mustapha ke ciki ta tarar har anyi masa allurar barci cikin turancin daya daga cikin Likitocin yake gaya mata ta zauna nan kusa da shi ta kula da shi yana tashi ta kira su, Mustapha ya kwashe awanni yana barci kafin yabuɗe idonsa karaf idanunsa kan fuskar Sumayya saurin mayar da idanunsa yayi ya rufe yai shiru kamar mai barci, komai yasoma dawo masa a kwanyarsa "Nooo!!!" yafaɗa da ihu tareda mikewa duka a lokaci ɗaya, wuyan Sumayya ya shaka "Ke kika ja komai ina Aimanah ina Ammi?" Sumayya idanu zare ta kasa magana saboda shakar dayayi mata wanda takeji kamar za'a zare mata rai magana takeso tayi ta roke sa yayi hakuri ya kyaleta amma ta kasa, dan kansa ya saki wuyan nata tareda haɗata da bango, gefan gadon ya koma ya zauna tareda dafe kansa yana fitar da numfashi da sauri sauri "Ina wayata?" yafaɗa yana kallon Sumayya data koma can gefe ta tsugunna har sannan tana rike da wuyanta, mika masa wayan tayi ta koma nesa da shi ta tsaya tana kallon sa, lambar Ammi ya loda sannan ya danna call, bugun farko Ammi ta ɗaga wayan gabanta na faɗuwa ganin kira da wata lamba ta wani kasa "Ammi kiyafemin" abinda Mustapha yafara faɗa kenan bayan Ammi tai picking call ɗin "Mustapha kaine Alhamdulillah Allah na gode maka" Ammi tafaɗa da muryar kuka "Ammi ina Aimah" "Tana nan kalau" "Ammi gida zan tawo" "Mustapha ka zauna ka karasa abinda yakaika India kwanki fa suka rage maka" "Ammi Aimah fa bazan iya zama anan ba Aimah ba" hmmm Ammi taja numfashi tana goge hawayan tausayin ɗanta dasuka zubo mata "Karka dawo Mai babban suna ka zauna kamar yanda nace maka Aimanah tana nan har kadawo" "Shikenan Ammi zan zauna ki turomin lambar Aimah na kira naji muryarta" Ammi ta katse kiran ta ɗora kanta saman kujera ta fashe da kukan tausayin Mustapha, "Mustapha kadawo hayyacinka a kurarran lokaci yamzu Aimanah tazama ta wani" kuka tayi sosai sannan ta mike ta fita daga ɗakinta zuwa na Momy, Mustapha yamaida kansa ya kwanta saman bed na asibitin yanajin zuciyarsa kamar zata fasa kirjinsa ta fito, wata iriyar soyayyar AIMANA ce ketasowa tun daga kasan zuciyarsa "Ammi bazan iya ba, bazan iya jure zama anan ba Aimah ba, mikewa yayi yana kallon Sumayya data haɗa kai da gwiwa ta zafga tagumi "Ke kisa a sallameni gida zan koma" asanyaye tamike ta fita shi kuma ya koma ya zauna yana tinanin irin hukuncin da zai yankewa Sumayya, saki shine babban abinda zuciyarsa ta amince dashi A can gida kano kuwa gaba ɗaya hankalin Amarya yatashi da kyar ta lalubi hijab ɗinta ta saka tana kokarin fita daga ɗakin Murjana ta shigo ɗakin, kallo ɗaya Amarya tayiwa Murjana ta ɗauke kai tana tsaki "Mama ina zaki?" "Wajan boka Tsito zani komai ya warware" "Mama dama kin zauna basai kinje ko ina ba ni na tone komai" "Na shiga uku" Amarya tafaɗa tana ɗora hannu aka "Murjani ke kika mana wannan ɗanyan aikin, na shiga uku ni naja'atu Allah ya wadaranki Murja" Amarya ta fice fuu daga gidan gaba ɗaya. Aimanah da Abas soyayya suke sosai da sosai ko yaushe suna manne a waya ayyuka sun masa yawa sosai sakamakon karin girma daya samu a wajan aiki hakan yasa bai zuwa kano sosai sai da waya, tuni Aimanah tafara aiki a ɗaya daga cikin gidan redion dake cikin garin kano, sosai tamaida hankali wajan aikinta, yau agajiye ta dawo daga wajan aiki gaba ɗaya bata jin daɗin jikinta kamar mai zazzaɓi haka takejin jikinta wanka kurum tayi ko abincin dare bata tsaya taci ba ta wuce ɗakinta zata kwanta barci, harta gama addu'ar kwanciya barci ta lulluɓa da blanket taji alamar shigowar sako wayarta, da sauri ta ɗauki wayar tana murmushi "Abas farin Masoyi" tafaɗa afili tana kokarin cire key na wayar _"Fatan alkhairi tareda fatan kina cikin aminci ina mai neman afuwa bisa tarin ɗimbin zunubin dana aikata a soyayyarki_ mamaki tayi ganin bakuwar lamba da bama ta wannan kasar ba goge massages ɗin tayi taja tsaki ta koma ta kwanta tana mai cewa kilama saɓanin number aka samu, Abas ne ya kurata suka sha soyayyarsu har tayi barci sannan ya kashe wayarsa ya kwanta. Mustapha gaba ɗaya baya cikin nutsuwarsa gaba ɗaya hankalinsa yayo gida kano nageria, sam yafita harkar Sumayya ayanda yaso tun acan zai yanke igiyar auransu gaba ɗaya amma yakasa saboda tausayinta da yaji ya jinkirta sai yadawo gida,yau cike yake da murna da ɗokin gobe zai bar india zaiyi ido huɗu da sarauniyarsa Aimanah murmushi yayi sanda ya tuna Aimah ya tina tilin tex masaages daya ke aika mata amma bata taɓa dawo masa da reply ba, shi duk azatonsa fiahi tayi baisan cewa batama san shi bane, ita kuwa Aimanah ko sau ɗaya bata taɓa kawowa wai Mustapha nw ke aiko mata da sakonni ba waɗanda tana ganin shigowarsu wasu ta karanta wani ma ko buɗewa batayi zatayi delate ɗinsa, dan yanzu ba kowa a gabanda da zuciyarta sama da Abas wanda takewa wani irin so, sosai take son Abas a yanzu a cewar Aimanah yanzune tai soyayya, soyayyar Mustapha datayi a baya ba soyayya bace idan ta haɗata da ta Abas, Abas ɗan soyayya ne ya iya soyayya da tattalin mace kusan ko yaushe suna jone a waya motsi kaɗan ya kirata ya ce yayi kewarta, yau Aimanah ba inda taje kasancewar lahadi ce tana gida bata fita, azaune suke a falo itada Mahh suna kallon Arewa 24 Aimanah na tsotsar alawa ahankali kamar wata karamar yarinya Mahh ta kalli Aimanah tai murmushi "Hmm Abas zai sha yarinta dan Allah jibi yanda kike ta tsotsar alawa mai tsinke kamar wata yarinya" Aimanah ta ɓata fuska kamar mai shirin kuka "Mahh nifa yarinya dika shekaru na basufi goma sha bafa" "Kice ma baki shekara ba" Mah tafaɗa tana maida hankalinta kan shirin da ake haskawa a arewa, wayar Aimanah tayi kara alamar shugowar kira kallo Mah tay taga hankakinta ba akanta yake ba hakan yasa tai pickin call ɗin "Hello Masoyi" Aimanah ta faɗa a hankali tana satar kallon Mahh "Masoyiya ya kike, kawau naji kewarki na kiraki" "Kewa niko bana kewarka saboda ko yaushe kana maƙale a zuciyata" "Nima haka, gabana faɗuwa yake Masoyiya yanzu Kanol ya kurani zamu shiga daji, tsoro nakeji gabana faɗuwa yake Aimanah ji nake kamar wani abu zai sameni nifa gani ma nake kamar mutuwa zanyi....😰 [2/13, 4:44 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi Na Goma Sha ɗaya* "Mutuwa kuma? haba masoyi tabbas mutuwa wajibi ce akan dukkan mutum bawa mai numfashi amma bazaka mutu yanzu ba, masoyi bansan ka da sarewa ba kaida kake karfafawa wasu gwiwa kuma yau kazo da wannan maganar insha Allah nasara ke tare da kai, katashi kai shiri ka haɗa rundunarka ku tafi Allah yana tare dakai Masoyi" "Na gode masoyiya kin karfafa mun gwiwa, duk na sare inda zamuje ba sarvice kwana uku zamuyi ki kularmin da kanki, ki adanamin soyayyata can kasan zuciyarki, kiyi barci sosai banda tunani mai yawa, Ina fatan duk sanda kika tina ni kimin addu'ar samun nasara" "Insha Allah nasara na tare damu" kashe wayar yayi naja ajjiyar zuciya ina ɗago kaina muka haɗa ido da Mah wacce bansan tsawon lokacin data shafe tana kallona ba "Masoya, in anyi magana kice ke yarinya ce gashi har kin iya kalaman soyayya" "Mahh" Aimanah ta faɗa cike da kunya, mikewa Aimanah tayi tabar wajan tana dariya, Mah tabi Aimanah da kallo tana mamaki, ada in wani yagaya mata Aimanah zata so wani bayan Mustapha zata karyata amma hukunci na ubangiji yau ga Aimanah nason wani mutum fiyeda son datayiwa Mustapha. Mustapha sun sauka lafiya a nageria kai tsaye jirginsu a kano ya sauka daga airport texzi yasamu ta kawo su har gidansu wanda baida nisa sosai da airport, ba wanda yagawa dawowarsu hakan yasa kowa na gidan ya shiga murna da dawowar Mustapha banda Amarya da damuwa gaba ɗaya ta mamayeta har ƴar rama tayi na fargabar halin da zasu shiga itada Sumayya Murjana ba karamar ɓarna tayi masu ba hatta aikin da tayiwa Alhaji Kamal saida tabi inda suka binne ta tone komai shima gaba ɗaya ya canza mata, yau tsaka sai ganin Sumayya tayi a ɗakinta saida gabanta yafaɗi ganin Sumayya "Ke kuma yazaki shigo min nan basai ki wuce gidanki ba, ni basai naje mu gaisa ba" "Mama Musty fa cewa yayi na zauna zai neme ni" dafe kai Amarya tayi tana faɗin "Shikenan na shiga uku tamu ta kare" Murjana dake zaune a gefe dariya tayi tareda saka eair pies a kunnanta tana faɗin "Kuna ruwa" "Allah wadaranki Murja ubangiji ya kwashe maki albarka yasaki a masifar da kika samu" "Mama wannan wacce irin addu'a ce? kefa uwa ce in kina mata irin wannan baki saiya wahalar da ita" "To Sumayya wahala ta nawa kuma ai wahala yanzu ta fara itace fa ta tone duk abunda muka bunne" "Duk da haka Mama, Murja ai yarinya ce yarinta ke ɗawainiya da ita dan Allah ki daina mata addu'a irin haka" Mama bata sake cewa komai ba taja hannun Sumayya suka wuce cikin ɗakinta. Mustapha kai tsaye ɗakin Ammi ya shige yayi sa'a kuwa tana gida lokacin tana tsaye jikin firij zata ɗakko ruwa taji an rungumeta ta baya bata zaci Al Mustapha bane duk zatonta Shaheed ne tasan shine mai mata haka "Shaheed Allah ya nuna min randa zaka girma ka daina min wannan rungumar" jin ansake kankameta ba'ayi magana ba ga wani kamshin turare na daban da takeji yasa tasan ba Shaheed bane "Hmm Amadu sakeni karka saka na faɗi" "Ammi kin manta dani, Allah yasa ma baki cire ni a jerin yaranki ba" Ammi goran ruwan hannunta ta saki ya faɗi a kasa tai saurin janye hannunsa daga jikinta ta juyo tana kallon Mustapha "Mai babban suna saida kabaro kasar nan kadawo ko?" "Ammi na gama fa, bakiyi farin ciki da dawowata ba ko? nasani nasan za'ayi haka duba da tarin laifukan dana aikata" "Nayi farin ciki sosai Yayansu na kuma godewa Allah daya dawomin dakai lafiya, ina matar taka?" ɓata fuska Mustapha yayi ya juya zai fita Ammi ta rike hannunsa "Ammi ba matata bace sakinta zanyi" "Karka soma Mustapha ban amince kasaki Sumayya ba kaci gaba da zama da ita sannan ka zage wajan addu'o'i da Azkhar" "Ammi bazan iya zama da ita ba, Ammi Aimanah tagama school ko?" "Mubar maganar Aimanah jekayi wanka kazo kaci abinci mayi magana daga baya" Mustapha jiki sanyaye ya fita daga gidan zuwa gidansa, gidan yayi kura sosai, dole yadawo gidansu ɗakin Ahmad yai wanka ya shirya, yasa Surayya itada Shaheed su gyara masa gidan, kafin ya gama wankan Ammi ta haɗa masa abinci ya zauna taci abincin sosai saboda yayi kewar abincin gida nageria sosai, yana gama cin abincin yayi hamdala yana kallon Ammi "Ammi muyi maganan Aimanah so nake naje na ganta na wanke kaina" "Mustapha" Ammi ta kira sunansa tana kallonsa "Kayi hakuri bazan munafunce ka ba, Aimanah tasami wani auranta ma kwanaki suka rage" da sauri ya mike tsaye yana kallon Ammi yakasa cewa komai yai tsaye kan Ammi baki buɗe so yake yayi magana amma yakasa saboda wani abu daya tokare masa a makoshi, yakoma ya zauna saman kujera ya kifa kansa saman teble, wani irin bugu zuciyarsa keyi harta Ammi dake zaune kusa da shi tanajin bugun zuciyarsa jin shiru tsawon mintina Mustapha bai motsa yasa Ammi ta ɗora hannunta a kansa, ɗagowa yayi ya kalli Ammi idanunsa sunyi ja sosai kamar garwashi Ammi hankalinta ya tashi sosai tasani daman tasan za'arina wai ansaci zanin mahaukaciya tasan tsananin son da Al'mustapha kewa Aimanah, "Al Mustapha kayi hakuri kaɗau abin nan a matsayin kaddara sannan kasa a ranka dama can Aimanah ba matarka bace" "Ammi kaddara kaddara fa kika ce, sai in tsaya ina nan a raye a aduniya ina numfashi wani can wawa ya aure Aimanah,Allah kar yasa naga wannan rana, da wani ya auri Aimanah ina raye gara na mutu nabar duniya, Ammi wannan kaddarar tamin nauyi bazan iya ɗauka ba, Ammi gayamin wacce addu'a akeyi mala'ikan mutuwa yazo ya ɗauki ran mutum" Ammi ta mike tsaye tareda kama hannun Mustapha ganin yanda jikinsa ya fara rawa, kalaman dake futowa daga bakinsa kaɗai sun tabbatar mata da Mustapha baya hayyacinsa, bedroom ɗinta ta kaisa ta zaunar dashi gefan gadonta ta ce "Mustapha kwanta ka kaji barci inka tashi zakaji sauki a zuciyarka" "Ammi barci bazai iya ɗaukata a wannan yanayin ba vani aron makullin motarki naje wajan Aimanah" "Mustapha bazan bari ka fita a wannan yanayin ba ka kwanta nace" bazai iya masu da Ammi ba hakan yasa ya kwantar da kansa saman filon Ammi "Kayita hasbunallahu wan'?wani'imal wakil zuciyarka zatayi sanyi" yajima yana kwancan yana ambaton hasbunallahu har yaji salama a zuciyarsa Ammi tana can Kicin ya lallaɓa ya fice daga gidan. ......Aimanah a shirye ta fito daga ɗakinta gidan shiru ba kowa, kowa ya wuce wajan aikinsa ita kaɗai ya rage a gidan itama yau dan bazata fita da wuri ba, tana fitowa compount taga shigowar motar Ammi fasa karasawa wajan motar tata tayi ta nufi motar Ammi, motar Ammi tinted ce na waje baya ganin na ciki amma na ciki yana iya ganin na waje, buɗe murfin motar Aimanah tayi cikeda ɗokin ganin Ammi kasancewar sun jima basu haɗu ba "Ammi Wellcome" Da sauri Aimanah tayi baya tareda dafe kirjinta, tsaye tayi tana kallon Musty dake jingine jikin mota yana aika mata da zazzafan kallon love wanda ya kusa tarwatsa zuciyarta, tabbas yasani bata jure irin wannan kallo ko acan baya bare hanzu, juyawa tayi zata bar wajan da sauri yakira sunan ta "Aimaah" cak ta tsaya ta kasa tafiya na ƴan sakanni can kuma yaci gaba da tafiya da sauri ta nufi motarta, tasa makulli zata buɗe motan Al'Mustapha ya ɗora hannunsa saman nata ya zare car key ɗin daga jikin mirfin motar ya zirasa a aljuhunsa ya harɗe hannayansa a kirji yana kafe Aimanah da lumsassun idanunsa masu kama dana maijin barci.....✍🏻 *Saura kiris adaina fitar da Littafin Aimanah za'a daina posting ɗinsa a ko wanne group sai Aimanah fans group da Aimanah comment section idan har kinsan kinason cigaba da karanta Aimanah maza yi save ɗin wannan lambar 07039793439 kiyi magana ta whatssapp zatayi adding naki a group ɗin da zaki karanta hankalinki kwance batare da ko sisinki ba* [2/13, 4:44 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na goma sha biyu* .....Aimanah kasa jure kallon nan tayi hakan yasa tayi kasa da idanunta gabanta na cigaba da dukan uku uku "Aimaah nasani ni mai laifi ne a wajanki, kiyi hakuri ki yafe min bada sanina hakan ta faru ba" "Kamin shiru ka kyaleni Al'Mustapha ka bar nan wajan bana sonka bana kaunar ganinka" Aimanah tafaɗa tana rushewa da kuka "Aimaah please stop craying kukanki kin sani yana taɓan zuciya kiyi shiru muyi magana ta fahimta" "Na fahimceka? wazan fahimta? kai can a baya mai yasa katafi ka barni da ciwo a zuci sai yanzu kadawo kace na fahimceka, Musty nariga nawuce level ɗinka kaje can ka zauna tareda masoyiyarka wacce ka guji kowa sabida ita" "Aimah komai zan faɗa maki bazaki gane ba ki bani dama a karo na biyu a zuciyarki" "Zuciyata a yanzu babu kai Abas ne aciki shine mai mulkin zuciyata dan Allah indai zancan soyayya ne yakawo ka kabar nan" "Bazan bari ba Aimah yazama dole ki tsaya muyi magana, ashe daman har akwai wani da zuciyarki zata so bayan ni?" "Kasa a zuciyarka ban taɓa soyayya da kai ba, lokacin dana so ka bansan zaƙi da ɗacin so ba, kasani a yanzu bana sonka! bana sonka!! bana sonka!!! nafaɗa bana kaunarka" taci gaba da kuka tareda kwasa da gudu ta shige falo ta rufo kofa, da sauri yabi bayanta kafin yakai harta sakawa kofar key da karfi yake buka kofar yana faɗin Aimah Aimah please ki buɗemin kofa" "Bazan buɗe ba kafita kabar mana gida mugu macuci mayaudari azzalumi" Aimanah ta dafe kirjinta datake ji yana wani irin bugawa da sauri sauri "Mai yasa kadawo yanzu? mai yasa zaka shigo rayuwata a yanzu, Abas kazo ka ɗauke ni nadaina ganinsa" haka tayita surutai bayan ta kulle kofar tana jiyo sa yana rokonta amma takasa cewa komai kuka take sosai na tausayin kanta. Abas yau kwanansu uku kenan cikin jeji sun fafata da ƴan ta adda sosai an kashe wasu dayawa a cikinsu yayin da wasu suka ji mugayan raunika, Abas yana cikin waɗanda sukayi rauni sosai a hannunsa hakan yasa suna dawowa bareck aka yi asibiti da su, ya kira wayar Aimanah tafi a kirga amma bata shiga hakan ba karamin tada masa hankali yayi ba, ko raunin hannunsa bai ɗaka masa hankali ba kamar rashin shigar wayan Aimanah, Anty Ummi ya kira ita ta tura masa lambar Mas'ud shima yinin ranar yanata kiran lambar tana shiga amma ba'ayi pickin ba, kallon matashin sojan dake tsaye kusa da shi yayi ya ce "Joseph ɗakko mota ta a gida ka kaini kano" "Amma oga kano yanzu dare yayi kafin mu isa sha biyun dare zatayi fa" "Umarni na baka ba cewa nayi ka bani shawara ba" Abas hanunsa nannaɗe da bandeji ya shiga mota Josepha kejan motar sai Hilux guda ɗaya mai cikeda sojoji da zasu masa rakiya zuwa kano, kamar yanda Joseph yafaɗa kuwa basu shiga kano ba sai sha biyu da minti ashirin da biyar na dare, hotal suka kama Abas yana ɗaki ɗaya tareda Joseph dake kula fa shi, Daran ranar idon Abas baiga barci ba, hankalinsa a tashe yake da tuna nin mai ya sami wayar Aimanah, kafin bakwai na safe yagama shiri yata shi Joseph dake barci ya na gaya masa yata shi zasu fita "Sir zan iya yin wanka?" "Kasan zakayi wankan ka kwanta kanata barci, tashi mu tafi bana da lokaci inmun dawo ka yi wankan kafin mu wuce jigawa" Joseph haka ya tashi suka wuce, karfe takwas na safe a kofar gidansu Aimanah tayiwa Abas, mai gadi yasa yayi masa sallama da Aimanah, lokacin Aimanah fitowarta kenan daga ɗakin barcinta sakon Baba Sunusi ya isketa tana da bako a waje, daga farko cewa tayi bazata fita ba a zatonta Al'Mustapha ne sai da Baba sunusi ya ce mata Abas ne, cikeda ɗoki ta shiga ɗakin Mah tafaɗa mata Abas na waje yana kiranta "Aimanah da safan nan, karki fita ki cewa Mus'af ya shigo da shi falon baki" Aimanah tafaɗawa Mus'af ya fita ya shigo da shi, Aimanah Kicin ta shiga tana gayawa Haule mai aikinsu a dafa mata shayi yai kayan kamshi a soya plantein da irish ra fice zuwa falon baki, Joseph ta hanga tsaye a kofar ɗakin ta karasa, Joseph ya kame tareda sara mata "Good morning Madam" "Morning ya kake ya aiki" bata jira amsar saba tayi wuf ta shige ɗakin sabida ta ɗokantu taga Masoyinta abincin ruhinta, cak taja ta tsaya tana kafe sa da idanunta wanda shima itan yake kallo da sauri ta karasa kusa da shi ta ɗora hannunta saman hannunsa mai ciwo idanunta na zubar da kwallah ta ce "Kalbie maiya sami hannunka?" "Ina wayarki?" mirmushi tayi tai saurin tashi ta koma saman kujera ra zauna tana sake kafe sa da kallo, ita gaba ɗaya ma ta manta da wata waya tun shekaran jiya data kashe wayan saboda masifar nacin kiran da Al'Mustapha keyi mata "Ki bani amsata Hayatie" Aimanah turo baki tayi gaba tareda kauda kanta daga kallonsa "Ni nafara tambayanka fa Kalbie maiya sami hannunka?" "Harbi ne ba wani babban ciwo ba" "Wayata ta sami matsala ta ɗauke gaba ɗaya, Yah Mansur yace zai turomin da wata" shiru Abas yayi yana kallonta yanayin yanda tayi magana kawai jikinsa yabasa ba gaskiyya ta faɗa masa ba hakan yasa ya ce "Mus'af baya nan ne, inhar wayarki lalacewa tayi nasan bazai taɓa bari yinin ranar ta wuce batare da ya canza maki ba" "To karya nayi kenan?" Aimanah tafaɗa da damuwa a fuskarta ganin ya ramfo ta, "Ni na isa na ce Hayatie tayi karya kawai ban karɓi maganar bane" "Kaci abinci?" Aimanah ta waske da masa tambaya "Banci ba banama jin yunwar idanuna kawai so suke suga Sarauniyata mai mulkin zuciyata" mikewa Aimanah tayi tana faɗin "Ina zuwa" ta fice daga ɗakin yabita da kallon yana jin wani yanayi na daban na shigar sa, saurin rintse idanunsa yayi tareda kwantar da kansa saman saman kujeran, zuciyarsa na bugawa da matsanancin soyayyar Aimanah. Kicin Aimanah ta koma ta taya Haule suka gama shirya komai ta sa Haule takaiwa Abas ita kuma ta koma ciki wajan Mahh, Abas godiya ya yiwa Haule ya umarce ta data ɗibarwa Joseph ta bashi ya koma mota yayi breakfast, kusan mintina goma sha sannan ta koma ɗakin har sannan baici komai ba daga cikin tarin abubuwan da aka ajje masa, kwansa kwance saman kujera ta shiga ɗakin, buɗe idanunsa yayi ya kalleta sau ɗaya ya maida idanunsa ya rufe, "Kalbie baka ci ba wai?" "Bazan iya ciba ko zaki bani a baki, hannun dama na keda ciwo" Gaban teble taje ta haɗa masa shayi mai kauri a Mug ta zuba irish da plantein a plate ta koma kusa da shi ahankali take basa yana karɓa sai wani narke mata yake kamar wani karamin yaro, baici dayawa ba ya ce "Hayatie am full" hararan shi tayi ta ɓata fuska "Umm uhmm Kalbie baka koshi ba jibi fa kaɗan kaci" "Allah na koshi Hayatie rabon dana ci abinci da yawa irin haka tun kafin na haɗu da ke, daga sanda kika shigo zuciyata na kasa sakewa naci abinci da yawa kullum far gaba nake da tsoron kar wani yazo yamin kwace bazan iya wani sakewa naci abinci sosai ba sai randa aka mikamin ke gidana, daga ranar inaga abinci sai kin rinka kwacewa" sosai Aimanah tayi dariya kafin ta ce "Naji to yanzu shanye wannan tea ɗin" tafaɗi haka tana ɗora masa Mug ɗin a kan laɓɓansa baki ya buɗe tana basa a hankali harya shanye gaba ɗaya, sun jima suna hira kamar bazasu rabuba kafin yatafi bayan yaje sun gaisa da Mah. Ammi ta kalli Al'Mustapha dake lulluɓe cikin bargo sai rawar sanyi yake ta ce "Dan Allah Mai babban suna katashi kasha tea ɗin nan, sai lallashinka nake kamar wani karamin yaro, rabon da kaci wani abu fa tun jiya da safe" "Ammi kimin addu'a mutuwa zanyi Aimanah ta guje ni ta manta dani bata son gani na" "Al'Mustapha ka kiyaye ni kai wanne irin mutum ne mai taurin kai da rashin magana, sau nawa na gaya maka ka futar da Aimanah a ranka kananun mutane kake so mu zama" Mustapha ya lumshe idanunsa tareda buɗe su akan fuskar Ammi ya ruko hannunta ya ɗora a kirjinsa "Ammi taɓa kiji yanda zuciyata take bugawa na tabbata son Aimanah shi zaiyi ajalina" Ammi ta zauna gefan gado ta runtse idanunta tareda saurin ɗauke hannunta daga kirjin Mustapha tai shiru, Ahmad dake tsaye a ɗakin shima zaman yayi kusada Mustapha yana kallon sa cikeda rausayawa. Amarya gaba ɗaya abin duniya yadame ta ganin yau kwana biyu kenan Sumayya na gidan Mustapha baice masu komai ba, kullum cikin zulumi take da fargabar karya kawo masu takardar saki "Mama ina kika sakamin wayata ne?" Murjana ke faɗa tana tsaye kan Amarya "Ban sani ba shegiya ƴar banza" "Amarya ki daina zagina karna rama wata rana kiji haushi, ni ki bani wayata Mas'ud ne bazan daina waya da shi sabida shi zuciyata ke so kuma shi zan aura, shi yayi min alkawarin indai na tone komai zai aure ni" Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un Murjana daman sabida Mas'ud kika tona mana asiri" Amarya ta shaki wuyan Murjana tana kokarin kasheta da sauri Sumayya ta shiga tsakanin su ta ɓanɓare Murjana da ga jikin Amarya da kyar wacce tuni ta fara fitar da numfashi "Allah ya isa tsakani na da ke, ubangiji ya kwashe maki albarka kuma yanda kikai sanadin asirinmu ya tonu kema bazaki taɓa samun masa'ud ɗin ba ko zanyi yawo tsirara bazan taɓa bari ki auri wannan munafikin ba" "Karki bari mana badai shiga bokaye bane nima zanbi mu zuba ni dake sai na sake tarwatsa komai, saina faɗawa Abba har zuwa kike wajan boka kina kwana da shi mazinaciya" Murjana tafaɗi tana haki, Sumayya hannu tasa ta ɗauke fuskar Murjana da mari "Bakida hankali Murja uwar tamu kike kira mazinaciya a gidan ubanki tayi zina" "Gidan ubanki dai karki sake zagina dan wallahi zab iya ramawa" fuu Murja taja mayafinta dake ajje kan hannun kujera ta fice daga gidan gaba ɗaya, Amarya ma mayafin nata ta ɗauka ta fice daga gidan aka bar Sumayya ita ɗaya a ɗakin, karan farko kenan da Sumayya taji ɗakin yayi mata kunci ta fito tsakar gida kawai ta tsinci kanta da shiga ɗakin Ammi, tabi ɗakin da kallo karan farko kenan data taɓa shigowa sashin Ammi, babban falo ne tangameme daya sha manyan royal cheir daga can gefe kuma babban danning ne sai wasu set na kujerun acan gefen dama na ɗakin kofofi biyu ne manne a bangon ɗakin daga kudu alamar ɗakuna ne sai ɗaya kofa daga ɓangaran yamma nan ma da alama ɗaki ne, sau biyu tana sallama sai ana uku taga an buɗe ɗaya daga cikin kofofi biyun dake jere da juna, Ammi ce ta fito da murmushi a fuskarta ta ce "Sumayya sannu da zuwa kin biyo mijinki ko?" Sumayya ta sunkuyar da kanta kasa tana murmushi ta tsugunna har kasa ta gaida Ammi "Tashi tashi Sumayya zona shiga dake yana ɗakin Ahmad bayajin daɗi shiyasa ma bance ki koma gidanki ba" ɗakin data fito suka koma ciki inda ta hangi Mustapha kwance yana barci "Kinga ma ashe yayi barci, yagayamin yace wai ki zauna saiya neme ki, ki shirya yau ki shiga gidanki ki zauna shima yana ta shi zan tattara sa ya bar min gida kuje can kuyita zaman hakuri" Sumayya mirmushi kawai tayi batace komai ba duk da kuwa wani daɗi daya ziyarci zuciyarta bata jima sosai ba ta koma sashin Amarya ta tattara nata ya nata ta koma gidanta. Yau tun safe Abas ya kira Aimanah yana hanyar dawowa daga jigawa zai zo su gaisa a hanya yake zai koma Abuja, Cus cus ta dafa masa wanda yaji kayan lambu da zallar tsokar naman sa, sai jus na kwa kwa data haɗa masa wanda yai sanyi sosai komai ta kai falon Daddy inda yake saukar bakinsa ta ajje sannan ta shiga wanka, sosai tayi kwalliya ta haɗe cikin shuwariski lace ɗinkin street gwon wacce tabi jikinta kamar a jikinta telan ya haɗa kayan babban mayafi tasa sanda ya kirata a waya ya ce gashi a waje "To ka shigo" ta faɗa a shagwaɓe "Uhmm uhmm kizo dai ki shigo dani" kashe wayan tayi ta gayawa Mah Abas yazo, tana fita compound yana shigowa gidan tsayawa tayi cak a inda take harya karaso wajan "Barka da rana sarauniyata" "Barka dai sarki mai mulkin zuciyar sarauniya" dariya sukayi alokaci daya suna kafe junansu da kallo, sun jima suna kallon juna irin kallon nan da bahaushe ke kira da kallon kuda, Aimanah ita tafara janye idanunta tayi gaba tana faɗin "Kashigo ku gaisa da Mahh" bayanta yabi suka gaisa da Mah sanan Aimanah ta masa jagora zuwa falon bakin Daddy, abincinta zuba masa kinci yayi dole saita basa da kanta "Allah Kalbie bazan baka ba wancan karan ma saboda hannunka na baka yanzu kuwa alhamdulillah hannu ya warke, kariga da kasan haramcin hakan" hannu yasa yaɗau cokalin yafara cin cuscus ɗin bayan yayi bisimillah sai santi yake mata tareda zuba mata surutu harya cinye bai sani ba😂saida yakai spoon bakinsa yaji ba komai ya kalli plate ɗin gabansa, atare suka kwashe da dariya, sun jima suna hira kafin ya mike zai tafi tayi masa rakiya har wajan gidansu inda yafaka motarsa, wata haɗaɗɗiyar mota ce ta faka a kusa data Abas ma mallakin motar ya fito, gaban Aimanah ya faɗi ta kafe wanda ya fito daga motar da kallo ganin yanda ya wani rame, Abas dake magana ya lura hankalin Aimanah baya garesa ya kalli inda take kallo da sauri yadawo da ganinsa ga Aimanah yaga dai har sannan gayan take kallon gyaran murya Abas yayi wanda yasa Aimanah saurin juyowa ta kalli Abas tana kokarin saita kanta ya watso mata tambayya "Wane wannan ɗin" Aimanah tayi kasa da kanta jikinta na rawa ta kasa kallon Abas "Kiyi magana mana kinmin shiru, ok na fahimta masoyinki ne Al'mustapha.....? *Saura kiris adaina fitar da littafin Aimanah za'a daina posting ɗinsa a ko wanne group sai group na Aimanah real fans group 1 and 2 Idan har kinsan kina son cigaba da karanta Aimanah kuma kinsan zakiyi comment maza yi save ɗin wannan number 07039793439 da Mamin Humaidah kiyi mata magana ta whatssapp zatayi adding naki a group ɗin dazaki karanta hankalinki kwance batare da ko sisinki ba* [2/13, 4:44 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na goma sha uku* *Wannan page ɗin gaba ɗayansa sadaukarwa ne ga masoya Book na Aimanah Musamman ƴan Aimanah Real fans group two* Aimanah takasa cewa komai haka ta kasa haɗa idanu da Abas batayi aune ba taga harya shiga mota yana kokarin tada motansa, da sauri ta buɗe front seat ta zauna batare data rufe murfin motar ba "Fita fitarmin a mota Aimanah" ɗagowa tayi tana kallon Abas dayake fitar da huci kamar wanda yayi dambe, tuni idanunta suka soma zubda hawaye "Haba Kalbie shikenan daga na kalli wani waje sai kace wani nake kalla, abar shi ma wani nake kalla shine mai, nidai nasan kaine nake so ba wani ba, kada kallon wani ya ɓata mana wannan lokacin, kai nakeso kaine a zuciyata, bazan taɓa kallan wani kallo irin na soyayya bayan kai ba, Abas kanada matsayi mai girma a zuciyata taya zan iya kallon wani kallon soyayya bayan kana kusa dani?" "Aimanah ki fitarmin a mota" yafaɗa a zafafe, Aimanah rufo mirfin motar tayi ta gyara zamanta cikin motar tana kallon cikin idanunsa wanda bata hango komai ciki sai zallar rigima da ɓacin rai "Abas ni kake kora a motarka" "Na korekin kije kici gaba da kallon masoyinki gashi can ya shiga gidanku" "Shikenan" Aimanah tafaɗa ranta ɓace, kokarin buɗe murfin motar tayi amma yaki buɗuwa ta lura ansawa motar scurity, "Ka buɗe na fita" hannunsa yasa saman hannunta, lokacin da hannunsa ya haɗu da nata taji wani ƴar a gaba ɗaya jikinta "Aimanah yanzu saiki iya tafiya ki barni a wannan yanayin?" "To yaya zanyi dakai Abas na gaya maka gaskiyya kaki fahimta, ka buɗe min na fita" "Hayatie zuciyata tana maki wani irin mahaukacin so wanda ni kaina bazan iya misalta maki kalar saba na riga na faɗa irin sosai ɗin nan, zuciyata tayi wata irin bugawa a sanda naga kina kallon wani bayan gani a tsaye gabanki, shiyasa nan take zuciyar tawa ta bani Mustapha ne, ina da kishi sosai akan abinda nakeso ki kiyaye karki sake kallon wani namiji inhar muna tare" "Bazan sake ba Hayatie kaine rayuwata gaba ɗaya, bazan sake ɓata ran masoyi naba wanda ya wanke duk kan wata damuwa a zuciyata, Hayatie ina tsananin so da kaunarka kaunar danake maka takai matakin da bana iya kallon ko wanne ɗa namiji, Kasani a raina kai nasa ba wanda nake gani, ko ruwa na ɗeba ciki zan sha kai nake ganowa, kaine mahaɗin rayuwar da duk zanyi kasan sai da kai, hannunsa dake cikin nata ya damke sosai yana kallon idanunta "Muyi alkawari Hayatie duk runtse duk wuya ɗayanmu bazai rabu da ɗayansa ba" "I promise" "Yes Hayatie I promise" hannu suka haɗa tareda jinjinawa, ta zare hannunta a hankali daga nasa "Idan katafi yau sai yaushe?" "Sai ranar ɗaurin auranmu" "Haba dai dafa saura dayawa" "Sati uku yayi saura ai, bazan ma iya ba abaya ma bana sati banzo kano ba bare yanzu da naga ana neman yi min fin karfi" "Ka kwantar da hankalinka ba wanda zai iya kwace maka ni" "Na kwantar irin kamar kayi bako ya mutum ɗin nan" dariya suka yi sosai kafin Aimanah ta fito da wayarta taɗan masa kusa da shi kaɗan ta masu picture, guda ɗaya tayi masu ta sake saita wayan tana kallonsa "Captein smile" murmu sawa yayi ta masu hoto ta maida wayanta kan cinyarta "Amma zaka halarci dinner ɗin Uncle Yunus" "Bazan zo ko wanne event ba amma zanzo wajan ɗaurin aure" "Shikenan ka sauka lafiya" tafaɗa bayan ta buɗe door na motar ta fita tana ɗaga masa hannu harya yice daga layin. Aimanah sanda ta shiga gida Al'Mustapha ta tarar tareda Mah tana duba lesika da alama shiya zo mata da su, Aimanah Mah kawai tayiwa sannu da gida ta wuce tana gafda shiga ɗakinta Mah ta mata magana "Zo nan Ummu Aimanah" dawowa Aimanan tayi ta zauna kasan carfet gaban kujerar da Mah ke zaune "Mah gani" Mah bata kulata ba taci gaba da duba lesukan gabanta can tayi magana "Sunyi kyau Al'Mustapha, tagaya maka kuɗinsu" Al'Mustapha ya shafi kansa kana ya ce "Mah na biya kuɗin gaba ɗaya harna Anty Hasanah" "Masha Allah Musty muna godiya Allah yakara arziki mai albarka ya cika buri" "Ameen ameen" Mustapha yafaɗa yana kallon Aimanah, Mah kallon Aimanah tayi kana ta maida ganinta ga Al'Mustapha "Wai banga kun gaisa ba, ince dai ba gaba kuke ba" Aimanah ɓata fuska tayi tareda kautar da kanta can gefe batace komai ba "Mah Aimanah ta daina kulani rannan dana zo ma kofa ta rufe ta hanani shigowa" "Aimanah mai kenan gaba kike da shi" "Mom ni..." kuka ne kawai ya kwace mata ta mike da gudu ta shige ɗakinta, shiru Mustapha yayi, har can cikin ransa yakejin kukan nan na Aimanah, Allah Allah yake Mah ta tashi a wajan ya shiga ɗakin Aimanah kamar kuwa Mah tasani ta mike ta faɗin "Mustapha bari na adana kayan nan a ɗaki nasan Hasana tana gafda zuwa gidan nan tun safe ma nake saka ran zuwanta kilama gajiya ce ta hanata fitowa ta sha zaman jirgi" Mustapha baice komai ba yabi Mah da kallo harta shiga bedroom ɗinta, yana ganin shigarta kamar wani ɓarawo ya yi wuf ya shige ɗakin Aimanah, kwance ya sameta saman bed tana ta faman kuka kamar ranta zai fita, tsayawa yayi kofar ɗakin yana kallonta har kasan ransa yake jin kukan nan nata, harya shigo ɗakin ya zauna gefan gadon bata sani ba tana faman kuka kukan daya rasa na menene "Aimaah daina kukan nan please na gaya maki bana son kukanki" da sauri ta ɗago tana kallon sa batace masa komai ba ta maida kanta taci gaba da kukanta, saman gadon ya hau sosai ya zauna harya saka hannu zai taɓata ya tina haramcin hakan da sauri ya mike ya sauka daga gadon, saboda wani abu daban da zuciyarsa ta ɗarsa masa "A'uzubillah" yafaɗa a hankali yana kokarin fita daga ɗakin sai dai kuma yakasa fita ɗin saboda yanda yakejin zuciyarsa ya tsaya baki kofa "Aimahh dan Allah ki daina kukan nan na roke ki, ki tsaya muyi magana naji ya yarda yanzu bakya sona ai ko ba soyayya daman can ni ɗan uwanki ne" "Ni kafita bana son ganinka" bai sake tsayawa yace komai ba yasa kai ya fita yayi sa'a Mah bata falon hakan yabasa damar fita daga gidan gaba ɗaya, tun daga wannan ranar Aimanah bata sake saka sa a idanunta ba har aka fara bikin Uncle Yunus, Uncle Yunus kanin su Mahh ne babansa wan babansu ma ne, a gidansu yata shi wajan Ana, ana ita ta rikesa bayan rayuwar iyayansa sanadin haɗarin mota tun yana ɗan shekara goma sha biyu. Gobe ne yinin biki wanda Ana zata gudanar a wani babban wajan taron biki dake nan cikin garin kano, gaba ɗaya ƴaƴa da jikoki muna gidan Anah anata shan chatter mun cika falon Ana da surutu baka jiyo muryar kowa a wajan sai tawa data Rumaisa babbar ɗiyar Anty HASANA da kaɗan na girmi Rumaisa yan shekaru ne na bata, tamu tazo ɗaya sosai shiyasa duk sanda suka zo nageria muna jone, Ammi ta fito daga bedroom ɗin Ana tana mitar mun cika masu kunne "Ai ga kaji can guda hamsin Alhaji muntari ya aiko dasu daga kasuwa suje su gyara" Anty Hasana ke faɗar haka da itama ta fito daga ɗakin Anan, da sauri Anty Ruma matar Yaya Muneer ta mike zata fita, Anty Ummi ta ruko hannunta tana dariya "Wallahi bazaki fita ba dake za'ayi aikin nan, haka ɗazu ma daga Mah tace mu ɗora abincin rana kika gudu gidan, Zeenatu saida aka gama sannan kika dawo ci" "Kai Anty Ummi harda sharri" Ruma tafaɗa tana kallon Ammi data tsare su da idanu, gaba ɗaya su Aimanah suka fita wajan gidan inda Ana ke wanke wanke a hankali suke gyara kajin sunata hira ana tsokanar Aimanah itama yau bikinta saura sati biyu, Aimanah ɗago kan dazatayi taga shigowar Al'Mustapha shida Yaya Mas'ud sai Surayya a bayansu tana rikeda manyan ledoji guda biyu, Mas'ud da Al'Mustapha sunyi kyau sun haɗe cikin Blue ɗin shadda sai walkiyya take a kallo na farko inkayi masu zaka zata ƴan biyu ne sai ka sake kallonsu sannan zaka banbance kamaninsu, kallo ɗaya nayi masu na kauda kai ina taɓe baki, Rumaisa ta taɓoni na ɗago ina kallonta ta nuna min su Mas'ud "Kalle su Yah Aimanah sun birgeni sunyi kyau sosai" "Ke kikaga haka ni basu birgeni ba, ni rukemin nan" na mika mata naman dake hannuna muka cigaba da wanke su da lemon tsami, ina jiyo sun Mustapha da Anty Hasana sunata hira nayiyo an kama sunana yafi a kirga a maganar tasu har muka gama wanke kajin muka shiga dasu gidan Hajja Kande wacce ita aka bama aikin abincin bikin gaba ɗaya, washe gari aka ɗaura aure muka sha hotuna da ƴan uwa da abokan arziki na kusa dana nesa, Abas bai sami halartar ɗaurin auran ba mundai yi waya da shi yana hanyar zuwa kano, wajan karfe biyu anata tafiya wajan yinin kusan kowa ya tafi gidan shiru Aimanah kaɗai da Rumaisa suka rage a gidan suma jiran karasowar Abas suke, wayan Aimanah tayi kara harga Allah tayi zaton Abaa ne amma tana kallon screen na wayar taga Uncle Yunus ne tai picking call ɗin ranta ɓace "Yauwa Aimanah ga wata mota nan a waje nayi mantuwa a ɗakina ki duba zaki ga babban leda fara da kaya a ciki ki ɗakko ki kawo za'a taho min dasu, badan taso ba taje ta ɗau ledan ta fita, mota ɗaya ta gani a layin hakan yasa ta nufi motan ta kwankwasa glass na motan aka buɗe murfin motar ganin ba wanda ya fito a motar an barta tsaye da leda a hannu ranta ya kara ɓaci daman cike take fam da rashin shigowar Abas garin da wuri, juyowa tayi zata koma cikin gidan da sauri Mustapha ya fito daga motar yana jinjina taurin kan Aimanah so yayi ta shigo motar yatafi da ita, "Aimah" cak ta tsaya jin ankira sunanta da Aimah tasan ba kowa bane sai Al'Mustapha, ledar hannunta ta dire a wajan ta shige cikin gidan da gudu, Musty dariya yayi tareda karasawa ya ɗauki ledan ya koma mota yana dariya ganin shirin su baiyi ba, wajan uku na yamma Abas ya zo wayanta kawai ya kira Aimanah itada Rumaisa suka fito, motoci biyu suka gani a wajan da sauri wani soja ya fito daga motar dake gaba ya buɗe masu murfin kofar motar suka shiga, Abas na hakimce a bayan babbar motar sai dariya yake ganin yanda Aimanah ta ɓata ranta, ya kalli Rumaisa yana dariya "Barka da shugowa naija mutanan Qatar" "Yawwa barka Kalbie" Rumaisa ta faɗa tana dariyar itama, Abas leka fuskar Aimanah yayi yaɗan ɓata rai kaɗan "Sorry Hubbie na ɓata lokaci ko, jokob ne baya taka mota sosai har saida fa na karɓi tukin na rinka gudu kamar zan kifa" "Kai ko" Aimanah tafaɗa tana kauda kanta gefe, sanda suka isa wajan atare Abas da Aimanah suka jera zuwa ciki, sojoji guda biyu na gefansu dama da hagu, gaba ɗaya hankalin kowa yayo kansu, Al'Mustapha ma akan idanunsa suka shigo har suka zauna yana kallonsu, a cikin idanun Abas yaga tsantsar so da kaunar Aimanah, yanda yake kulawa da motsinta kaɗai abin burgewa ne, yana kallo ya buɗe mata lemu ya mika mata kaɗan tasha ta mika masa sauran ya shanye duka, kasa kasa suke magana suna dariya a kallo daya inkayi masu zaka gano su ɗin masoya ne na hakika take zazzaɓi ya rufe Al'Mustapha harya soma ganin duhu duhu Shaheed ya kira ya basa car key ɗinsa yace ya kaisa gida, Shaheed ya maida sa gida ko zama baiyi ba ya koma wajan bikinsa, Mustapha na shiga gidansa Sumayya tayi sauri ta tashi zata tare sa hannu ya ɗaga mata ya wuce ɗakinsa ya rufe da key ta ciki, wani iri yakejin kansa kamar zai raɓe biyu saboda azabar ciwon dayake masa, magani yasha ya kwanta barci yayi gaba dashi bai farka ba sai ana kiran sallar mangariba shima bugun kofar da akeyi ne yatashe sa, kofar ya buɗe Sumayya ya gani tsaye a bakin kofa tana sanye da hijab da alama sallah zata tada, "Naji ana kiran sallah ne shiyasa na buga maka kofa" tsaki yaja ya koma ciki ya shige bathroom ya ɗauro alwala ya fice masallaci, bai dawo daga masjid ba saida akayi sallar insha ya shiga gidansu, ya tarar tini Ammi ta dawo, gaidata yayi kana ya zauna kusa da ita yayi shiru "Da aka tashi na neme ka ban ganka ba da wuri ka tawo kenan?" "Kaina ke ciwo Ammi" Ammi kallon ɗan nata tayi tausayinsa fal cikin ranta, akan idanunta taga tahowarsa wanda ta tabbata saboda ganin Aimanah da yayi da wani ya haddasa masa barin wajan harma da ciwon kan, "Allah ya sauwake kasha magani?" "Nasha" yabata amsa da kyar yana dafe kirjinsa da lokaci ɗaya yaji ya masa wani irin nauyi, gyaran murya yayi ya buɗe baki zaiyi magana wani amai yatawo masa na zallar jini, gaba ɗaya Ammi ta ruɗe hankali tashe tayi wajan Al'mustapha wanda jiri ya ɗebesa ya zube kasa.....✍🏻 [2/13, 4:44 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na goma sha huɗu* "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" shi Ammi keta ambata hankali tashe, Alhaji Kamal da shugowansa gidan kenan yaji salatin Ammi atare suka shigo ɗakin shida Momy, cak Alhaji Kamal ya ɗauki Mustapha hankali tashe yayi asibiti da shi, Ammi da Momy suka bi bayansa a motar momy dan Ammi batada nutsuwar dazata iya tuki duk hankalinta yatashi gani take ma kamar kafin suje asibitin za'ace ya mutu. Murjana ta fito shirye tsab cikin shirinta na fita unguwa tana kallon Amarya batace mata komai ba har takai bakin kofa Amarya ta ce "Murja ina zakje ne yauma jiya fa baki kwana a gida ba" "Amarya ina ruwanki da inda zani gari zan shiga kuma jiya da ban kwana a gida ba naga ina gidan Kawarki maman Salim can na kwana tare da shi kinsan sun shigo kano" Amarya ta washe baki jin anyi maganar Salim "Masha Allah ƴar albarka abinda nakeso ki gane kenan, yawwa kiɗan masa wayo irin naku na yammatan zamani ki samo mana yan kuɗin jiya nace wajan boka kiri kiri yakimin aiki wai saina basa dubu saba'in" "Bakida damuwa ɗari ma zan kawo maki gobe inna dawo" "Yawwa ƴata shiyasa nake alfahari dake kin fuye min waccan Sumayyan data kasa taɓukawa kanta komai" Murjana sa kai tayi ta fita wajan gidan inda wata haɗaɗɗar mota ke fake, shiga tayi cikin motar, Salim yatashi motar yana aika mata da kallo "Kinyi kyau kaunata, yau dai ina fatan za'a bani dama na shiga koramar nan da jiya aka hanani shiga aka barni da zulumi" Murja dariya tayi tana gyara zaman mayafinta ta ce "Yau kam insha Allah zaka shiga can ciki ba shamaki duk da dai inajin tsoro bantaɓa yi ba" "Haba karkiji wani tsoro aiba da zafi zan maki ba, jiya na tabbata baki san harkar ba ganin yanda jikinki ke rawa, gaba ɗaya kin hanamin nutsuwa barcin danayi gaba ɗaya mafarkinki ne, yanzu ma fa saida nayi wanka da zan fito, bakiji yanda na kwaɗetu da naji zumarki ba, kinsan ku yan duma duma ɗin nan kunada wani sirri daba kowanne namiji ne yasan shi ba, shiyasa a kallo ɗaya dana maki randa mom ɗina ta aikani wajan Mom ɗinki na faɗa" Murjana dariya tayi tana kashewa Salim idanu "Yanzu to ina muka nufa?" "Gidanmu mana" "Wai kana nufin yau ma acan za muyi nifa kunyar Mom ɗinka nakeji" "Mom ai vatada damuwa, Dad ɗina ne masifaffe shi kuma baya ma kasar yana thailand kuma ta kofar baya zamu shiga gidan ba wanda zai san ina gidan ma bare a hanani morewa" Murja tayi shiru tareda kwantar da kanta saman kujerar motar, har suka karasa gidan bata sake magana ba, Salim da kansa ya buɗe get ɗin bayan ya shiga ya faka motar a ciki ya maida get ɗin ya kulle, buɗewa Murja kofa yayi ta fito suka jera kai tsaye zuwa ɗakinsa, babban ɗakine daya sha kayan alatun more rayuwa kamar wani ɗakin Amarya basu tsaya a falon ba kai tsaye bedroom ya wuce da ita ya zaunarta gefan gado yafara rage kayan jikinsa, yarage daga shi sai gajeran wando Murja gaba ɗaya kunya ta kamata ta rufe fuska ya zauna kusa da ita ya hata da jikinsa ya kama hannunta ya ɗora saman j ɗinsa, jikin murjana ya kama karkarwa saboda hannunta daya taɓa abinda bata taɓa gani ba, "Kinga nutsu muyi magana nawa ne farashin wannan ranar" Murjana jin anzo wajan da take bukata ta saki jikinta tana kallonsa "Nawa zaki biya?" "Zan biya farashi mai tsada indai kinmin abinda nakeso" Salim ya biya bukatarsa wacce yadaɗe yana fata da buri akanta, shi daman harga Allah ba auranta zaiyi ba, bukatarsa kenan, tun daga ranar yamaida Murjana tamkar matarsa sanda duk yaji bukatar kasancewa da ita waya kawai zai mata yaje ya ɗakkota in bukatarsa ta biya yadawo da ita gida da makudan kuɗaɗe da siyayya kala kala Amarya tayita rawa tana murna ƴarta mai farin jini. *Al'Mustapha* Ba wani ɓata lokaci likitoci suka karɓesa emargency sukayi da shi, Ammi kuka take sosai momy na rarrashinta, har sanda likitocin suka fito, Ammi bata tsaya jin abinda suke cewa Abba ba tabi gadon da aka turo Al'Mustapha zuwa word, zama tayi gaban gadon ta ruko hannunta cikin nasa, yayi firit fuskar nan tayi fayau kai daga ganin barcin dayake kasan bana daɗi bane, Aimanah tasa kafa ta zunguri Rumaisa dake barci "Allah Rumaisa in baki tashi ba zan gayawa Mah har yanzu bakiyi sallah ba takwas saura fa" "Anty ki barni nai barcin nan Allah na gaji sosai" "Ok saboda kin gaji bazakiyi sallah ba akan lokaci ba ni ma ai da gajiyar amma haka nayi sallan da asuba, ki tashi kona saɓa maki" Aimanah jin anbuɗe get na gidan za'a fita da mota tai saurin ɗaga labulan window ɗin ɗakinta, Mah ta gani da Daddy a mota zasu fita, da sauri tasaki labulan ta fita compound na gidan kafin ta karasa har sun fita sai Yah Mas'af da Ma'aruf tsaye fuskarsu fal damuwa "Yah inasu Daddy suka tafi da safiyar nan?" Aimanah ta faɗa tana kallon Yaya Mas'af, baice komai ba yaja hannunta zuwa cikin gidan "Yah kamin magana fuskarku fal damuwa nagani" "Kinga kwantar da hankalinki ba wata damuwa bace bafa, Musty ne ba lafiya yana hospital tun jiya da dare sai aman jini yake" Aimanah ta dafe kirji tareda fito da idanuwa "Musty fa" tafaɗa cikeda damuwa, hannunta ta cire daga na Mus'af ta shige ɗakinta, Rumaisa ta tarar a tsaye tana zagaye ɗakin tana ganin shigowar Aimanah ta rokota ta fashe da kuka "Anty wai Musty ne a hospital an rasa gane kansa sai aman jini yake yanzu Anty ta kirani tana kuka take faɗa min, kizo muje hospital ɗin" Aimanah hararar Rumaisa tayi ta koma gefan gado ta zauna tana danna wayarta Rumaisa na tsaya tana kallonta ganin ko a jikinta wayama take da Abas hankalinta kwance, Rumaisa ficewa tayi daga ɗakin a fusace tayi sa'ar ganin Ma'aruf zai tafi asibitin suka tafi tare, Mus'af duk ya damu jin Aimanah shuru a ɗakinta kusan awa bata fito ya laƙa ɗakin barci yasamu tana yi hankalinta kwance, shima hankalinsa ya kwanta duk a tunaninsa zata damu da halin da Misty yake ciki, shima shiryawa yayi ya tafi hospital ɗin, asibitin ya cika sosai da ƴan uwa kowa hankali tashe har saida likitoci sukayi magana aɗan ragu kana wasu suka dawo gida akabar Ammi momy da Mah sai Anty Hasana daketa shuga da fita wajan likitoci dan jin abinda ke damun Musty yanzuma tana zaune gaban babban likitan dake kula da Mustapha "Hajiya gaskiya ɗanki na tsakanin rayuwa da mutuwa zuciyarsa ta kumbura sosai da alama akwai wani abu da yake damunsa a zuciya mun dai yi kokari mun tsaida aman jinin dayake, sauran kuma saidai mu ɗorasa a magani sannan inya farka ayi kokari a rinka kwantar masa da hankali sannan duk wani abu da kukasan zai sanyaya zuciyarsa ayi masa kana a guji ganin wani abu da zai tada hankalinsa" "Ok Dr mun gode" ta fita daga office ɗin wayar Aimanah ta kira lokacin Aimah tashinta daga barci kenan taga kiran Antyn saida gabanta yafaɗi haka kurum takejin tsoron Anty Hasana sabida tasan masifar ta, "Hello Anty" Aimanah ta faɗa cikeda ladabi "Sannu Aimanah yanzu a faɗa maki Musty ba lafiya amma ki kasa zuwa kusan kowa yana wajan nan banda ke, to inkinga dama kiyimin fatan dankali ki kawomin nan bance dole ba sai kinga dama" bata jira tace komai ba ta katse kiran Aimanah sakkowa tayi daga saman gadon tana turo baki gaba ta shiga kicin, Haule ta taimaka mata suka haɗa fatan dankalin daya sha alayyahu ta shirya cikin doguwar rigan atamfa da babban hijab ta ɗauki basket ɗin data gama haɗa komai a ciki ta fita, bata hau motanta ba titi ta fita ta hau adaidaita zuwa hospital ɗin, bata sha wuyan samun su ba tasami Ammi da Anty Hasana a recepsion, Ammi ce kawai ta amsa gaisuwarta Anty harara kawai take aika mata tana tsugunne a gabansu ta kasa cewa komai tayi kasa da kanta daga ta ɗago suka haɗa idanu da Anty Hasana harara kawai take aika mata "Zaki tashi ki shiga kikai masa abincin ko bazaki iya ba?" "Anty kiyi hakuri" "Naki na hakura, nace bazan hakura ba gashi nan sai kije ki karasa shi banda ma ke Aimanah gida bata koshi ba a...." "Kai Hasana dan Allah ki rage masifar nan taki kina girma kina daɗa cin kasa, ke Aimanah shiga ciki ki bawa Mah abincin tana ciki" Ammi tafaɗi haka tana kallon Aimanah, jiki sanyaye Aimanah ta shiga ɗakin akai sa'a Musty na kallon kofa, da sauri ya mike zaune harya na neman faɗowa kasa saida Mah tai saurin rikesa ta gyara masa zaman jikin filo har sannan idanunsa na kan Aimaah da take gaida Momy, Mah ce ta soma fita daga ɗakin kafin Momy ba tabi bayanta, Aimanah na tsaye jikin gadon takasa cewa komai idanunta na kasa tana hawaya ganin yanda Mustapha ya rame sosai ya kara wani fari tas kamar wanda ba jini a jikinsa, "Aimahh zuba min abinci naci yunwa nakeji" hannunta na rawa ta mika masa plate ɗin data zuba fatan dankalin, jikinsa duk ba kwari hakan yasa ya kasa rike plate ɗin, kujera taja gaban gadon ta zauna ta rike masa plate ɗin yana cin abincin a hankali, harya gama ta basa goran ruwa ya sha batace masa komai ba, tana kallonsa ya gyara zaman sa idanunsa a kanta "Ya Musty na sani duk saboda nine ne hakan ta faru, kayi hakuri ka ɗauki kaddara daman can kasa a ranka ni ba matarka bace, tabbas har yanzu zuciyata na sonka amma son dana kewa Abas yadame naka ya shanye koda ace nafi sonka a kansa lokaci ya rigada ya kure mana bazan maida iyayena kananun mutane ba, kayi hakuri ka zauna da matarka ko ka auri Rumaisa" kallon Aimanah kawai yake yama kasa cewa komai saboda tsabar takaici wai Aimah ce yau take kallon idanunsa take gaya masa tana son wani sama da son datake masa har tana basa shawarar ya auri wata, "Shikenan Aimah naji na gode kuma da kika gayamin gaskiyyar dani na kasa fahimta na hakura dake har abada😭sannan bazan iya auran Rumaisa ba, dan Allah Aimah ki daina guduna mu koma Aminai tunda kin daina sona, guduna da wulakanta ni da kike yafi komai ɗaga min hankali" "Insha Allah na daina gudunka daga yau banida aboki amini sama da kai" Aimanah tafaɗi haka tana saka hannunta cikin nasa, saurin cire hannunsa yayi daga cikin nata yaɗan ɓata rai "Abas ya ɓata min ke ko?"haramun ne rike hannun wani wanda ba muharramin ka ba kin rigada kinsan haka" "Yah Musty nifa kaida yaya Mas'ud ba ku da bambanci a wajena" "Da bambanci Aimah ni da aure a tsakaninmu shi kuma ba aure a tsakaninku" "Hum mubar maganar nan aboki" "An bari gimbiyata" "Gimbiya kuma ba ruwana in Anty Sumy ta jika" dariya sukayi tare, Mas'ud da Anty Hasana da suka shigo tare saroro sukayi suna kallon Musty dake kyalkyala dariya "Da kyau douther aikinki yayi kyau kinsa gawa ta tashi" "My Anty nine gawar" Musty yafaɗa yana kallon Anty Hasana" Mustapha zare allurar dake jikin canuler ɗin hannunsa yana kallon Mas'ud "Kaga Aboki kira Dr yazo ya sallame ni gida zan koma" "Sannu majanun Ka koma gida mana tunda lailar ka tazo" "Hmm" kawai Mustapha yace yana mikewa tsaye ya fita recapsion, Anty Hasana ta kalli Aimanah ta taɓe baki ta fice daga ɗakin. Murjana ta kalli Salim daya fito daga wanka yana tsaye gaban madubi yana gyara kansa, "Nifa Salim inajin tsoron shan wannan kwayoyin da kake bani kar sumin illa nan gaba," "Haba ba abinda zasu maki nafa hana ɗaukar cikine am Dector bazan baki abinda zai zamo mana matsala anan gaba ba, auranki fa zanyi" Murja ta mike ta wuce ta gabansa zata shiga bathroom "kai yarin nan kifa daina juya min mazauna nan naki zan iya komawa fa" "Haba kai kama isa gida zan koma Abba da Yah Ahmad sun fara matsamin fa naga kwanan nan idanunsu a kaina yake musaman Yah Ahmad kasan gayan nan ɗan bala'i ne, yanzuma basai ka kaini gida ba a daidaita zan hau" harasa sawa yayi kusa da ita ya rungumeta a jikinsa yana mata raɗa a kunne dai dai sannan Mom ɗin Salim ta shigo ɗakin kallo ɗaya tayi masa ta ɗauke kai ta zauna gefan gadon nasa tace "Saketa to ta shiga wankan zo magana zamuyi kasan yau Dad zai dawo kasar nan inajin kuma anan kano zai sauka" Murja ta faɗa bathroom cikeda kunya shi kuwa Salim ya zauna kusa da Mom ɗinsa yana kwantar da kansa saman kafaɗarta. Abas ya kalli Hajiya datake buɗe kayan da Hajiya Maimuna ta kawo "Malam Abas kayan nan basuyi yawa ba kuwa"Abas yashafi kansa yana murmishi ya ce "Hajiya basuyi yawa ba duba da gidan daza'a kai kayan" "Shikenan Allah yasa albarka" hajiya tafaɗa, Allahji Abubakar Mahaifin Abas yashigo kallon tarin akwatinan da manyan manyan jakukunan dake zube a falon kallon kayan yayi ya zauna saman kujera "Hajiya wannan kayan fa kamar za'a buɗe babban store" "Kayan ɗanka ne yanzu Hajiya maimuna ta kawo su" buɗewa Hajiya tasomayi tana nuna masa "Masha Allah kaya sunyi Abas Allah ya sanya alkhairi" "Amin Baba" "Au kace Amin" dariya akayi gaba ɗaya, Abas yamike yana shirin fita daga ɗakin "Abas ina zaka barmin kayan nan anan, maza gayawa su Alhaji Habu da yamman nan suzo sukai kano" "Abba wai kai lefanma bazakaje ba?" "To inje inyi me Abas ga wakilai na nan su Alhaji Habu ma sun isa komai" Abas yafita batare daya ce komai ba, a ranar aka kai lefan Abas gidansu Aimanah tareda invitesion na ɗaurin aure a baban kwali lodi guda, sati biyu ya rage hakan yasa ta ko'ina shirye shirye kawai ake daga ɓangaran Abas harna Aimanah tuni Anty Hasana ta ɗauke Aimanah zuwa gidan ta dake Kabuga gyara sosai take mata tareda magani sanyi bata zuwa ko 'ina, ko aikinta ma ta daina zuwa ta ɗauki hutu, ta kara kiba da haske alamun hutu sun bayyana karara a jikinta Abas tunda yazo washe garin da aka kawo lefe bai sake zuwa yana Abuja yace sai ranar ɗaurin aure zai zo waya kawai suke ba kama hannun yaro soyayya sai abinda yayi gaba, Bawan Allah Mustapha ya kasa mantawa da Aimanah yanzu suna waya sosai ana gaisawa ba batun soyayya sai zumunci, a gidansa kuwa gaba ɗaya Sumayya ta kasa gane kansa yafitar sabgarta wataran saita kwana ta wuni ma bata saka sa a idanunta ba, ga komai ya tsaya boka cin kuɗinsu kawai yake aiki baya ci, dan sosai Musty ya rike addu'a musaman azkhar ɗin safiya da maraice baya wasa dasu kusan ko yaushe yana makale da wayarsa yana karatun kur'ani cikin haka ne yasami karin girma da canjin wajan aiki aka maidasa CBN bank reshansu dake legos, shi kaɗai ya tattara ya tafi bayan yayi sallama da Ammi tasa masa albarka, wata kalar rayuwa yake a legos mai ɗauke da kunci da damuwa baya zuwa ko ima sai office ɗinsa kusan duk abinda zai siya ma oder yake akawo masa har gida,ko yaushe ka gansa fuska ba walwala, cikin haka har yau yarage saura kwanaki uku bikin Aimanah shi baima sai ba, saida yakira Ammi suka gaisa take ce masa "Mai babban suna baza kazo bikin Aimanah bane?" kirjinsa ne yai wata irin bugawa da har saida ya rikesa "Zanzo Ammi yaushe ne?" "Ranar Asabar ne mai zuwan nan" baice komai ba ya katse kiran ya jingina kansa da jikin kujera hawaye suka fara zubowa daga idanunsa kifa kansa yayi saman teble ɗin dayake kai yafara kuka a hankali, kuka yayi sosai kafin yafara ambaton Allah a zuciyarsa tareda fatan Allah yasa hakan shi yafi masa alkhairi, Anan kano kuwa sosai aka fara shirye shirye ba wasu event zasuyi ba dinner ce kawai ranar juma'a washe gari a ɗaura aure a wuce da amarya jigawa ranar lahdi Hajiya zatayi nata yinin litinin su wuce Abuja, inda amarya zata tare sosai abas ya gyara gidansa ya zuba komai na bukata bai bari su Aimanah sunyi komai ba duk da nacin da yaya mansur yayi amma yace subar komai shi zaiyi, gida yayi kyau sosai Anty Ummi data je ta gano ranar da zasu tawo kano sai yaba gidan take a jirgi ma ta cika Mansur da surutu duk akan gidan, yau Juma'a tun yamma kowa keta shirye shiryan tafiya tafiya wajan dinner da za'a fara karfe bakwai, waje yayi kyau sosai musamman ango da amarya kowa ka gani yana cikin farin ciki dangin ango basuda yawa sosai kusan dangin Aimanah su suka fi yawa a wajan anci ansha an gyagije amarya da ango sun rausaya wajan goma na dare aka tashi saboda gargaɗin da Daddy yayi kan kar ayi dare, Aimanah gaba ɗaya batajin daɗi misamman dataga ba Al'Mustapha a wajan dinner dan har Sumayya tagani a wajan, hakan yasa suna dawowa ta shige ɗakinta ta kullo ta zauna gefan gado tana danna wayarta Musty ta kira, Mustapha dake kwance ɗakinsa ya kasa barci ganin kiran Aimanah yai picking call ɗin da sauri "Yah Musty" kawai saita fashe da kuka "Aimah kuka kuma kukan me kike a wannan daran daya dace ki kasance cikin farin ciki daran da nine yaka mata nayi kuka" "Yah shine bakazo wajan dinner ba" "Bazan iya zuwa ba Aimah na ganki da wani nayi nadamar zuwa garin nan ma inaga jirgin safe zanbi na koma inda na fito" "Yaya kazo na ganka" da sauri yamike daga kwancan daya ke ya zari car key ɗinsa dake ajje saman firij ya fito, dai dai zai fito daga gidan a mota ita kuma Sumayya ta shigo bai tsaya ba kamar yanda take tsayar dashi yayi gaba, Kiran wayar Aimanah yayi ta fito compound na gidan inda yake zaune kan daya daga cikin fararan kujerun daya gani a wajan da alama wasu ne suka tashi a wajan, gidan yayi shiru kusan kowa yayi barci musamman daya kasance lokacin sanyi ne ko ba barci zakayi ba saika dangana da ɗaki, Aimanah tana hango Mustapha ta karasa wajan da gudu ta tsugunna ta fashe da kuka, shima kukan yake a haka Anty Hasana ta karaso wajan ta tarar dasu "kukan me kike, kukan munafurci kona yaudara?"wuce ciki kafin naci ubanki anan wajan salon ki saka ciwonsa yatashi muzo muna karasa biki a hospital, kai kuma ka wani zo gabanta kana wani kuka kamar karamin yaro Allah ya kaimu gobe zanyi magana da Alhaji kamal ɗin aure za'a sake maka" tana gama faɗar haka taja haunnun Aimanah suka wuce ciki, Wai akace rana bata karya sai dai uwar ɗiya taji kunya hakance ta faru yau waje waje yayi manyan mutane ta ko ina an taru ana kokarin ɗaura auran Abas da Aimanah liman ke kira ina waliyan amarya dana ango a matso kusa za'a ɗaura aure, Alhaji Abubakar ya matso kusa sukayi ido huɗu da Alhaji Farouk mai naira, hannu yasa yana nuna Prop Faruk mai nera fuskar Alhaji Habu ba walwala ya ce "Faruku maiya kawo ka wajan bikin ɗana" "Habu kai dai zance mai kazo yi wajan ɗaurin auran ƴata" "Kana nufin Abas ƴarka zai aura?"inko har hakane adakata adakata nace liman kar a ɗauran wannan auran na rantse da Allah ɗana bazai taɓa haɗa jini da naku ba Faruku...✍🏻👩‍🦯 [2/13, 4:44 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na goma sha biyar* Prop cikeda damuwa ganin yanda idanun mutane yadawo kansu ya ce "Habu abinda yafaru ya rigada ya wuce iyayanmu ne sukayi mu bazamu biya bashin gabar dasukayi ba" Alhaji Abubakar daya ɗauka da zafi huci kawai yake ya kalli Amininsa Habu ya ce "Alhaji Habu auran nan bazai yuwu ba zoka ɗaura ma Abas aure da ƴarka Habiba yanzu" "Alhaji in rai yaɓaci hankali fa baya gushewa komai yafaru a manta baya mun riga mun tara mutane kuma ni bazan ɗaurawa Habiba aure ba rana tsaka batare da saninta ba" "Haka kace" Alhaji Abubakar yasaɓa malum malum ɗinsa ya fice daga masallacin mutane suka bisa da kallo a dai dai sanda Abas da tawagar abokansa suka karaso anan Babansa ke gaya masa ba wannan ɗaurin auran yaje ya nemi wata, nan take Abas ya faɗi kasa akayi hospital da shi Prop tsabar bakin ciki kasa cewa komai yayi sai bin kofa da yayi da kallo baya ma jin abinda ke faruwa a wajan shidai kawai yaji sanda Akace fatiha aure yaɗauru tsakanin Al'Mustapha Kamal sareena da Aimanah Faruk mai nera, kokarin faɗuwa Alhaji Faruk yake da sauri amininsa Alhaji Kamal ya rukosa shida Ya Muneeer suka saka sa a mota Muneeer yaja zuwa gida, tuni labari yakai gida kan abinda yafaru Ma'aruf ne yakai labarin hankali yatashi sosai musamman Aimanah sanda taji labarin bada Abas aka ɗaura aure ba faɗuwa tayi sumammiya Anty Hasana ta zuba mata ruwa ta tashi tunda ta tashi take kuka taki cewa komai ta kira wayar Abas yafi sau talatin ba'a ɗaga ba,Mus'af kamar ya kaiwa Ya Mansur duka haka yaji dan shine silar wannan ɗaurin auran, Mah hankali tashe ta sami Prop a ɗakinsa tana kuka "Prop kasan abinda kayi kuwa yaya zaku ɗaura mata aure da Mustapha ya zaku jefa yarinya a masifa" "Dan Allah Aisha ki sarara min nima bansan da auran ba kinsan halin masifar dana shiga lokacin da Alhaji Habu ya wulakanta ni a gaban mutane, Mansur ne ya ɗaura auran Aimanah da Mustapha bani ba kije kiyi masa faɗa ni ki kyaleni da abinda yadaman" a fusace Mah ta fita daga ɗakin zuwa Compound inda Mansur ke tsaye shida sauran mazan da basu gama watsewa ba hannunsa kawai taja zuwa ciki har ɗakinta ta shiga da shi ta zaunar dashi gefan gadonta ta zauna a kasa "Mansur maiyasa kamin haka mai yasa da kayi fushi bakai tunanin mazai faru ba ina Aimanah ya Aimanah zata iya kishi da wannan yar matsafan kana fa ganin halin da ake ciki yauahe ma aka samu Musty ya farfaɗo" "Mah kiyi hakuri kaina ya kulle ne narasa mafita mahaifin Abas yayi fushi bansan maiya taɓa haɗasa da Daddy ba, kuma jiya naga Mustapha da Aimanah na kuka da daddare bayan mundawo daga dinner nayi zaton ko har yanzu tana sonsa" "Ni ba zancan so nake ba abinda zaije yadawo nake dubawa" "Mah muyi addu'a da fatan alkhairi sannan kisa ma auran nan albarka, ki goge fuskarki kar Ammi taga kukan nan naki bazata ji daɗi ba zata zaci bakison ƴarki ta auri ɗanta ne" da sauri Mah ta goge fuskarta sabida abinda Mansur ɗin yafaɗa gaskiyya ne, Ammi ta shigo ɗakin hankalinta tashe sai yanzu taji labarin abinda yafaru sabida bata gidan anan ta kwana gafda za'a tafi ɗaurin auran ta tafi gida sabida ta kira wayar Mustapha sau ba adadi bai ɗaga ba shiyasa taje ta gano lafiya, kuka take sosai tareda yiwa Mansur faɗan abinda yayi. Al mustapha na tsaye gaban closet yama rasa kayan da zai saka haka kurum baya son zuwa gidan su Aimanah yaya zaiyi ya zaiji yau idan yaga Aimanah a matsayin matar Abas ba shiba shifa sam baiso ma Ammi ta tarar da shi a gidan ba, karan da wayarsa tayi yasa ya saka hannu ya ɗauki wayarsa ganin lambar Shaheed kaninsa yasa yai picking call ɗin "Hello" Mustapha yafaɗa Shaheed cikeda ɗoki ya ce "Yayanmu albishirinka" "Kai ni sa'anka ne, kirana kayi kace an ɗaura wa Aimanah aure" "Allah ba haka bane, kiranka fa nayi na maka Allah ya sanya alkhairi an ɗaura auranka da Yaya Aimanah" da sauri ya zauna gefan gado yana dafe kansa "Shaheed zan saɓa maka" "Shikenan Yayanmu in an kawo ta gidanka ka yarda" Shaheed ya katse wayan, kafin Musty ya ajje wayar kiran Mas'ud ya shigo, a sanyaye yai picking call "Majanun da mace ne ni dana rangaɗa guda ango ango" "Kaima ka kira ka tsokane ni ko to duk kwayi ku gama gidan bikinma nafasa zuwa" "Ko baka zo ba ai zamu kawo maka amaryar anjima duk da itama ance tana can kwance ba lafiya koma dai maine kwa haɗe anjima" ajje wayar yayi ya mike zai saka kaya wani kiran ya sake shigowa tsaki yayi bai ɗaga kiran ba yaci gaba da saka kayansa sau uku ana kira bai ɗaga ba baima duba ba yaci gaba da shirinsa kiran dayake shigowa ba kakkautawa ne yasa ya ɗaga "Anty Ruma" "Ayirrrrrrrrrrrrrrrrri" Anty Ruma ta rangaɗa buɗar da saida tasa ya janye wayar daga kunnansa "Kai Anty Ruma karki kashe min dodon kunne na" "Ango mijin amarya aure ya ɗauru" kashe wayarsa yayi gaba ɗaya ya fita daga gidan zuwa gidansu Aimanah can gadon kaya, yana shiga ƴan uwa sukayo kansa ana ihun ango ango, Surayya kanwarsa harda rungumesa, Anty Hasana yabi da kallo ganin yanda take aika masa da wani kallo, karasawa yayi kusada ita ya gaidata "Burinka ya cika Musty" "Anty nifa ban gane ba, kema tsokanar tawa zakiyi" "Ni sa'arka ce dazan tsokane ka?" tsugunnawa yayi a gabanta sai kuma da sauri ya mike ya shiga can cikin gidan kai tsaye ɗakin Mas'ud ya shiga inda yatarar da Mas'ud da Mus'af na cacar baki kamar zasu daki juna "Ya'isa dan Allah" Musty yafaɗa yana rike Mus'af dake kokarin kaima Mas'ud duka "Sakeni malam ai duk bakinku ɗaya kun shiga kun futa an hana yarinya wanda takeso" "Mus'af zan naushi bakinka wallahi" Mas'ud yafaɗa yana tashi daga wajand daya zauna "Kadakenin mana maza tawo karka fasa, kunsa yarinya a masifa gashinan da safan nan sumanta nawa tunda taji labarin nan" "Ya'isa wai yaushe zaku girma ku daina wannan halin, kai Mus'af ka fita a idona fa tsorin idonka yayi yawa ka tsaya kana sa'insa da Mas'ud sa'anka ne?" "Mah kina gani fa..."Naga me kamin shiru" fuu Mus'af yafice daga ɗakin zuwa na Aimanah Ammi na tsaye kan Aimanah tana lallashinta kan tayi shuru ta daina kuka, Mus'af yazauna kusada Aimanah yana lallashinta kan tayi shuru taci abinci ta kwanta ta huta, "Mas'ud gaba ɗaya kun sani a duhu dan Allah warware min wannan lamarin" "Aure dai kasani an riga an ɗaura da kai" nan Mas'ud yai masa bayanin yanda abin yafaru, nan take Mustapha yai sujjadar shukkur yana godewa Allah bisa wannan ni'ima dayayi masa ba zato ba tsammani, mikewa yayi shima a nufi ɗakin Aimanah Ammi kaɗai ya tarar a ɗakin sai Aimanah dake can gefe kwance ta naɗe cikin blanket da alama sanyi takeji, Ammi taɗago ta kalli Mustapha farin cikin data hango shimfiɗe saman fuskarsa yasa ta murmusa ta ce "Ango masha Allah,ubangiji yasa alkhairi" "Amin ya Allah Ammi, nayi matukar farin ciki da wannan ni'imar da Allah yamin ba zato ba tsammani, sai dai Ammi nasani Aimanah yanzu bata sona ya zanyi" Ammi hannu ta ɗora samab laɓɓanta shiii ta nuna masa Aimanah dake kwance samab bed, zama yayi kusada Ammi ya ɗora kansa saman cinyarta ahankali ya ce "Ammi kinji gabana faɗuwa yake" "Yita karanta Hasbunallahu wani'imal wakil, da La'ilaha illah anta subahanaka inni kuntu minal zalimil" Aimanah dake cikin bargo zuciyarta ba daɗi ji tayi kamar ita Ammi take, nan take tafara ambaton Allah har barci mai nauyi ya ɗauketa, Ammi ce tafara fita daga ɗakin sakamakon kiran da Alhaji Kamal yayi mata, tana Fita Musty ya karasa inda Aimanah ke kwance ahankali yaja bargon ya buɗe mata fuska, ya sumbaci goshinta tareda faɗin "Alhamdulillah" yasake sumbatan labbata yafita a ɗakin yana faɗin "Sai mun haɗu a gidana Aimah" yana fita wayansa dake aljihu tayi kara da sauri ya cirota yai picking call ɗin cikeda ladabi ganin Abbansa ke kira "Zonan falon Dadddy muna jiranka" dam gabansa yafaɗi ahankali yataka har sashin Daddy, harya shiga ɗakin gabansa na faɗuwa can gefe saman carfet ya zauna kusa da Yaya Mansur ahankali yafara gaida Iyayansa dake zaune a wajan, Alhaji Kamal yafara magana "Nasan kariga da kasan abinda yafaru a ɗazu ga amana nan Mustapha dan Allah ka kula da Aimanah" "Insha Allah Abba" "Sai maganar lefe da inda Amarya zata zauna" "Abba abani zuwa gobe zan haɗa kayan, batun wajan zama kuma legos nakeson wucewa da ita" "Hakan bazaiyu ba Mustapha da ace bakada wata matar da zamu yarda da hakan amma yanzu in muka amince da haka mun zama masu son kanmu dole kayi adalci a tsakanin matanka karka manta Aimanah ba ita kaɗai ce matarka ba" Mah ke faɗar hakan "Hakane Mah shima abani zuwa gobe zanyi magana" "Shikenan Mustapha tashi kaje" Daddy ne yai magana a wannan karan, mikewa yayi ya fita, su kuma sukaci gaba da tattaunawa, Musty kai tsaye gidansa ya wuce yana shiga gidan ya tsaya cak yana karewa gidan kallo, gidan ba wani babban gida bane babban falo ne mai ɗauke da ɗakuna uku, ɗaga kai yayi ya kalli kafar benan da zai iya cewa bai taɓa hawa ba saboda ba kowa a ciki, bisimillah yayi yahau saman yana kare masa kallo, ahankali yake zagawa, babban falo sai ɗakuna biyu masu kallon juna gefe ga babban kicin, ko ina ya shiga ya duba komai dai dai kicin ɗinne kawai ba komai a ciki kamar wani ɗaki, wayarsa ya ciro ya kira babbar yayarsa Anty Halima "Ango" abinda ta ce kenan bayan tai picking call ɗin "Kai Anty kema kin sami labari kena" "Na samu mana Momy ke gayamin daman muna shirin futowa zuwa gidan Mah yanzu kuwa nan gida zamuyo" "Ok daman saman nan nake ganin Aimah ta zauna a ciki dana shigo ina dubawa kuma sai naga kicin ɗin ba komai ba'a gyara shiba kamar na kasa" "Ok bari na kira Anas kanin mijina yazo ya gani zai saka komai" "Ok saikin karaso" sakkowa yayi kasa shuru gidan kamar ba kowa kai tsaye ɗakin Sumayya ya buɗe ya shiga tana kwance tsakiyar gado sautin kukanta kawai ke tashi. *JIGAWA* kuka Abas yake hajiya na gefansa itama kamar zatayi kukan, kallon Alhaji take ji takeyi kamar ta tashi ta rufesa da duka "Wallahi Alhaji bakayiwa Abas adalci ba abinda yafaru can tsakaninku ne ba ruwan yaran nan aciki amma saboda taurin zuciya irin taka ka tarwatsa masu farin cikinsu kana ji yanzu an riga an ɗaura ma Aimanah aure da wani" Abas sake rushewa yayi da kuka kamar wani karamin yaro yamike yana zagaye a ɗakin hannunsa a ka "Na shiga uku Hajiya mutuwa zanyi wayyo ni wayyo rayuwata kaicona ni Abas, Baba maina maka daka min wannan abin" tsalle yayi tareda buga kafafunsa kamar mai shirin fareti ya kwasa da gudu zuwa ɗakinsa "Alhaji kayi magana mana" "Nace me, kinsan girman lefin da mahaifin Faruk yayiwa mahaifina kuwa, ba ruwanki a wannan lamarin ki zuba idanu kawai wallahi na kwammace Abas ya mutu daya auri yar Faruku" mukewa yayi yabar wajan Hajiya ta shiga ɗakin Abas inda ta samesa a tsaye sai zagaye ɗakin yake ya daina kukan amma idanunsa sunyi jawur "Abas banida kalmar da zan iya gaya maka face kayi hakuri" "Nariga na hakura Hajiya na ɗau kaddara amma kisani bazan taɓa aure ba tunda na rasa Aimanah haka zan kare rayuwata har abada babu wata mace da zata maye gurbin Aimanah a zuciyata da idanuna, zan bar garin nan jiya kanol ke gayamin suna na yana cikin waɗanta aka tura can kudancin kasar nan, addu'a nake Allah yasa acan asami wani ya hargeni na mutu kona huta da abinda nakeji a zuciyata" "Bazaka mutu ba Abas, zakayi farin ciki insha Allah zaka sami wacce tafi Aimanah komai" "Babu wannan matar Hajiya babu ita a nan duniya, banda ni musulmi ne nasan kaddara na yarda da ita da wallahi yau saina harbe kaina" "Subhanallah Abas karna kumajin wannan kalamin daga bakinka maza yi istigifari" "Hajiya zan tafi banajin zan kara zuwa gidan nan har abada sabida yau Baba ya nuna min iyakata" "Allah ya tsaremin kai Abas ubangiji ya kareka da kariyarsa yai ruko da hannayanka duk halin da zaka shiga karka manta da Allah ka ruki alkurni mai girma da tsarki zai sanyaya maka zuciya aduk sanda tai zafi" "Nagode Hajiya" Abas yafaɗa tareda rungume Hajiyar yana goge mata hawayan dayake zubowa daga idanunta har waje ta rakasa inda ya shiga mota tana kallon seteven yaja motar suka bar layin, data koma gida kuka tayi sosai na tausayin halin da Abas zai shiga kafin ya saba da rashin Aimanah addu'a take masa sosai ba dare ba rana [2/13, 4:44 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na goma sha shida* Al'Mustapha yakarasa kusada Sumayya ya zauna nesa da ita kaɗan kana ya ce "Lafiya kike kuka?" ɗagowa tayi kallo ɗaya ta masa ta sake maida kanta ta kwanntar tareda sake rushewa da sabon kuka "Ina tambayarki kinmin shuru" "Murja ce tamin waya ta gayamin an ɗaura maka aure da Aimanah" "Kuma sai tace ki zauna kiyita kuka" "Dole nayi kuka Musty ni kaɗai a gidanma ban isheka kallo ba inaga ace ga Aimanah a gidan nan nikam nasan tawa ta kare kilama sakina zakayi" ta sakko daga kan gadon ta rarrafo kusa da shi ta rike kafafunsa tana kuka "Dan Allah Yayanmu dan girman zatin Allah karka sakeni ina sonka wallahi Allah shine shaidata ina sonka ina kaunar zama da kai inka sakeni bansan yanda zanyi ba kilama mutuwa zanyi" "Ni nace zan sake ne, kinci albarkacin Ammi data hanani sakinki da tuni inma mutuwar zaki tini kina kabari, ki sani ko kaɗan bana sonki bana kaunarki dan dole nake buɗe idanu nake ganinki a gidan nan, kin ruguzamin duk wani tsarina da burina kin tarwatsa rayuwata, saidai alhamdulillah yau Allah ya maidomin da farin cikina burina tsarina Aimanah alhamdulillah duk wani mai bakin ciki sai dai ya mutu" "Kayi hakuri sharrin sheɗan ne da kuma son zuciyata, nidai na rokeka ka bani dama na gyara kura kuran danayi a baya" "Allah yasa ki gyaran" "Insha" tafaɗa tana ɗora kanta a saman kafadarsa. Prop ya kalli yaransa gaba ɗaya dake zaune saman carfet, gefe ɗaya Mah ce da surukanta guda biyu Anty Ummi matar yaya Mansur sai Anty Ruma Matar Yaya Muneer, Zayyad da Zaheed na gefe suna wasa da Noor ɗiyar Yaya Muneer, Aimanah da zazzaɓi ya rufeta na kan kujera ta lulluɓa da hijab ɗinta tana rawar sanyi "Dadd zazzaɓin nan yayi zafi sosai yakamata a kaita hospital" Mus'af yafaɗa yana taɓa jikin Aimanah "Yanzu ai ba aikinmu bane wannan Mus'af ka kira Mustapha ka gaya masa" Mus'af ya ɓata rai ya koma ya zauna yana danna wayarsa "Dad maiya haɗa ka Abban Abas tun safe ina cikin damuwa da son sanin abinda ya haɗaku" murmushi Daddy yayi yana kallon Ma'aruf dayai masa wannan tambayar "Bafa wani abu mai zafi bane ya haɗamu, Habu kauyanmu ɗaya dasu babansa manomi ne yayinda mahaifina Baffa yake makiyayi wata rana Baffa ya fita kiro da shanunsa yayi nisa sosai harya kusa isa burtali gajiya ta kama sa ya zauna karkashin bishiya danya huta barci ya kwashe sa kafin yatashi shanunsa sun shiga gonar Iliyasu manomi sun cinye gaba ɗaya shukar datake cikin gonar, hankalin Baffa yatashi sanda ya farka yaga ɓarnar da shanunsa sukayi yakaɗa su zuwa gida da kansa yaje har gida yasami Malam Iliyas yagaya masa ɓarnar da shanunsa sukayi nan fa Iliyas ya rinka masifa yana zage zage har abu yakaisu gaban mai gari, mai gari ya masu sulhu yacewa Malam iliyas ya kirga nawa ya kashe Baffa ya biya, Baffana ya amince zai biya komai amma cikin dare Malam Iliyas ya bankawa turken Baffa wuta shanunsa gaba ɗaya suka kone, sanda Iliyas ya bankawa garkan wuta makocin Baffa harɗo yana kallonsa hakan yasa ya sanar da mai gari ran mai gari ya ɓaci hakan yasa ya kori Iliyas da iyalansa daga kasar sa," "Dad aiba Baban Abas bane yakamata yaji haushinmu mune yakamata muji kullacesu danna tabbata ɓarnar da akayiwa Baffa ta wuce ta su" "Haka ne Ma'aruf saidai shi abinda yasa Habu ya kullacemu sanda aka kore su daga gari sanadin haka ciwo yakama Malam Iliyas na bakin cikin barin garinsa wanda ciwon ne yayi ajalinsa hakanne yasa Habu ya kullacemu" "Allah ya kyauta" Ma'aruf yace yata shi yabar ɗakin "Mah bani ruwa na sha" Aimanah tafaɗa tana daga kwance, da sauri Mus'af yatashi ya buɗe firij ya ɗakko ruwa mai saukin sanyi ya buɗe murfin goran ya ɗagota ya haɗata da jikinsa yana mata sannu yabata ruwan ta sha, ta koma ta kwanta tana sake lulluɓa da Hijab ɗinta, Mas'ud ya fita daga falon yana danna wayarsa, Mustapha dake kwance saman bed ɗinsa Sumayya na gefansa itama a kwance jin karar wayarsa dake ajje saman bedsate drower takai hannu ta ɗakko wayar ta mika masa "Lafiya zaka kirani da tsohon daran nan" Musty yafaɗa da sigar tsokana "Kaga nifa ba sa'anka bane yanzu surukinka nake dan haka ka girmama ni" "Sannu gwambo sarkin son girma" "Yawwa yanzu dai ga Lailarka ba lafiya Daddy yace kazo ka kaita hospital" da sauri Musty ya mike tsaye ya zari car key ɗinsa yafice daga ɗakin "Wayyo maiya sami reina da daran nan" "Ban sani ba" Mas'ud yafaɗa tareda katse kiran, Musty sosai yake taka motar yau kam ganin nisan gadon kaya yayi sosai duk da kuwa ba wani nisa tsakanin NNDC kwatas da gadom kaya, saida ya faka motar sa a compound gidan gaba ɗaya kunya ta kama sa daya ga kayan dake jikinsa shi kansa saida yayiwa kansa dariya, 3 kwata ɗin wando ne ja ajikinsa sai t shart baka wacce ta matukar kama jikinsa, yanzu a haka zan shiga gidan nan, mazewa yayi ya fito daga mota ya shiga babban falon gidan yana sanɗa yayi sa'a ba kowa a falon hakan yabasa damar wucewa sashin mazan gidan kai tsaye ya faɗa ɗakin Mas'ud, ɗakin ba kowa shuru buɗe closet ɗin Mas'ud yayi yafito da wandon juens blue yana kokarin sakawa Mas'ud ya fito daga bathroom tsorata yayi ganin mutum na kokarin saka dogon wando ya juya zai koma bathroom Musty ya gansa dariya nacinsa danya gano tsorata yayi ya ce "Kai dawo nine fa" ajjiyar zuciya Mas'ud yayi jikinsa duk a sanyaye danba karamin tsorata yayi "Allah yasakamin dan wallahi ka bani tsoro" "Kai wai bazaka rage wannan tsoron naka ba, a haka kuma kakeson Surayya cab duk taron matsorata in abin tsoro yazo gidan naku ba wani jarumi kaida ita duk tughether" "Dallah ajjemin wandona" "Naki na ajje ɗin, zoka ranaki ɗakin Aimanah nifa wallahi tsoron rikicinta nake" "OK gobema idam ankai maka ita tsoron nata zakaci gaba da ji kenan?" "Gobe kuma haba sai friday goben fa zan koma legos, inna koma zan samo hutun sati ɗaya nazo na more amarci na" "Angonci dai, ba kwaran kawai" "E naji nine ma kai, yanzu dai rakani dan Allah aboki" "Kasan Allah bazani ba tana ma sashin daddy" "Jar uba wai kana nufin can zan shiga a haka da kananun kaya amma ka cuceni da baka gayamin tun farko ba" "Ni na hanaka ka nutsu kenan ka tuna gidan surukai zaka zo" "Nidai rakani please" "Lalle naka wasa ne bari ma kaga na kwanta" "Dan Allah kataimaka ka rakani fitsarin nan zai zubo tsoro nakeji" gaba ɗaya suka tun tsure da dariya harda rungume juna "Kasan Allah aboki inna tuna rayuwarmu ta booding sainayita dariya ni kaɗai, yanzu dai muje na raka ka aramawa kura aniyarta" "Allah ya nunamin auranka da Surayya nazauna na bata labarinka da sanda ka shiga firgici sanda kaga aljana" dariya suka kuma yi Musty harda rike cikinsa dan dariya kamar yafaɗi "Allaj sarki Fahad ubangiji yai masa rahama oh rayuwa" "Ameen" Mas'ud yafaɗa dai dai sun shiga falon Daddy,Musty idanunsa akan kujera inda yake zaton Aimanah ce kwance ganin ana rawar sanyi cikin hijab kai tsaye wajan ya nufa bako kunya ko gaida su Daddy baiyi ba ya kalli Mus'af "Baka kallon rawar da jikinta keyi ka barta haka ba wani taimakon gaggawa" "Ba ɓangare na bane" Mus'af ya mike yabar falon, Musty buɗe hijab ɗin yayi ya ɗagota ta buɗe idanunta da sukayi ja taga shine komawa tayi ta maida kanta ta kwantar sannan tasa hannunta ta ture hannun Musty dake taɓa jikinta dayaji yai masifar zafi "Ka shika ni karka sake taɓani" tafaɗa lokacin daya sanya hannu yana kokarin tashinta zaune ɗan matsawa yayi kusada ita sosai bakinsa saman kunnanta ahankali kamar bayason magana ya ce "Ki tashi na kaiki hospital ko kuma na ɗauke ki da kaina ba ruwana da su Daddy suna kallona" da sauri ta mike zaune ta zira plate shoe ɗinta dake zube saman carfet ta mike tana kokarin faɗuwa yai saurin rukota jikinsa suka fita daga falon "Mah waisu kaɗai zasu tafi?" "Ko zaka bisu?" dariya Ma'aruf yayi ya fice daga ɗakin yana masu saida safe, Musty da kansa ya buɗe mata murfin motar ta shiga saida ya gyara mata zaman ta yamaida kofar ya rufe, ya zagaya driver seat, ahankali yake tukun mota yanayi yana kallonta hannunsa na cikin nata, yana kallonta cikeda kulawa, har suka kara wani babban pravite hospital dake zoo raod, lokacin jikinta yayi zafi sosai, yana rikeda ita a jikinsa, cikeda kulawa nurse suka karɓesu kai tsaye gado aka basu sanda Dr ya dubata yacewa Musty damuwa ce kawai sai fever jininta kuma ya hau dole sai an bata gado Musty ya siyo komai da suke bukata aka saka mata drip tuni barci yayi gaba da ita, Mustapha ya zauna gaban gadon saman farar kujera ya zuba mata idanu yana kallonta, Mas'ud ya kira ya sanar masa an basu gado yafaɗawa Mah, Mah ta kira Musty sukayi magana ko Anty Hasana tazo shi yatafi gida yabar Sumayya ita kaɗai, yace basai kowa ya zoba zai zauna zuwa safiya sai Antyn tazo, ajjiyar zuciya ya saki sanda ya ajje wayar shi gaba ɗaya ma ya manta da wata Sumayya a gida, yagama duba wayansa yaga ba lambar Sumayyan wayar Shaheed ya kira, Shaheed da baiyi barci ba yana falon Ammi yana kallon wasan kwallo yaga kiran Yayansu "Hello Yayanmu barka da dar" "Barka dai Autan Ammi, kaje ka gayawa Sumayya ta rufe ko ina ta kwanta bazan dawo ba ina Hospital Aimah ba lafiya" "Yayanmu maiya sami Aimah?" "Fever ne" "Ok Amma Abba ya rufe gida kasan doka ne, bari na duba in Murjana batayi barci ba saita kira ta a waya ta gaya mata" "Ok" Musty yafaɗa yai saurin katse kiran ganin Aimanah tana motsi [2/13, 4:44 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na goma sha bakwai* Saurin kallonta yayi zuciyarsa yaji tazo masa har wuya a fusace ya ce "Ki sani aurena dake ba saki inkinga na rabu dake to mutuwa nayi, kuma karki sake min irin wannan maganar idan na fusata komai zai iya faruwa inada kishi ki kiyaye yimin maganar wancan sojan" turo baki Aimanah tayi ta juya can taci gaba da barcinta, Mustapha kusan kwanan zaune yayi duk motsinta yana kula da shi har zuwa safiya, Anty Hasana ta fara zuwa tanata mita dan bataji ba tun dare da ita zata zo ta kwana da Aimanah, "wannan ai rashin kunya ne zaka zo asibiti ka kwana da yarinya kamar batada gata wama yasan iya abinda ka mata Allah yasa ma baka lalube mana ƴa ba," Musty baice komai ba yana gefe ya danna wayarsa haɗeda murmushi Anty tanata mita har Ammi tazo ita tasa Anty Hasana tayi shiru ta tisa keyar Musty yatafi gida yai shirin komawa legos, yana tafe a mota yana murmushi shi kaɗai musamman inya tina mitar Anty Hasana wai ya lalube masu ƴa, ina shi ina wannan aikin babba, yana shiga gida Sumayya ta taresa tareda tambayarsa ya jikin Aimanan "Da sauki" kawai yace ya wuce ɗakinsa yasa key, wanka yayi ya kwanta ramuwar barci, bai tashi ba har bayan azahar, sallah yayi yai wanka yasa Shaheed yasai masa tiket yai sa'a akwai jirgin dazai tashi zuwa legos karfe bakwai na daren ranar, gidan Anty Halima kai tsaye ya wuce jiya basu haɗu ba yanaso su karasa magana ga zancan haɗa lefe, yana shiga gidan yaran Anty Halima suka rinka murna ga Uncle Musty, Mustapha na son yara shiyasa ya rungume su yana tambayarsu school, harya zauna saman kujera yana tareda yaran saida Anty tamasu magana sannan suka fita daga ɗakin, ya cire hular kansa ya ajje gefe yana kallon Anty ya ce "Kin korar min yara" "Inba subar ɗakin nan ba bazasu barmu muyi abinda yakawo ka ba gashi kace yau zaka koma legos" Hmm yaja ajjiyar zuciya kana ya ce "Yau zan koma ya maganarmu ta jiya" "Narigada nayi masa magana yace anjima zaije ya gano wajan sai asan abinda za'ayi" "Ok yanzu dai ga ATM card ɗina nan ayi duk abinda yakamata bana son lissafi anyi kaza na kaza kawai ayi komai sannan kuyi magana da Anty Hasana gobe kuje ku haɗa lefe, Akaiwa Aimanah, Anty kusai kaya mai kyau da tsada kuɗin ciki zai isa komai insha Allah," "Bakada damuwa Ɗan uwa kawai dai kasan Anty Hasana akwai faɗa da mita" "Wai kema tana maki?" "To Anty wata kyale kowa ma yi masa take" Musty yai dariya kana yace "Kibita a hankali zaku gama komai lafiya" "Insha Allah" Anty ta faɗa, mikewa yayi sukayi sallama yatafi, asibiti ya wuce yatarar tuni an sallamesu sun koma gida, Anty yakira yana korafin mai yasa ba'a gaya masa ba "Sannu Mahd ubanmu" "Nifa Anty ba nan na dosa ba" kashe wayarta tayi bata jira jin mai zai ce ba, Musty yaso yaje gidansu Aimanah amma ya kyale saboda sunyi waya da Ammi take gaya masa gidan akwai mutane dole ya hakura haka yasa kai ya wuce legos batareda yasake ganin Aimanah ba. Abas wata irin rayuwa yake mai cikeda kunci da damuwa, gaba ɗaya bashida kuzari haka yakejinsa kamar wani mara lafiya ga ayyuka da suka saka sa a gaba, yau yana kwance a ɗakinsu dake barreck, Sulaiman ya kallesa ganin yanda ya kurawa waje ɗaya idanu yayi shuru yana dafe da kansa, Sulaiman dake zukar sigari ya matso kusada Abas ya mika masa sigarin "Ka karɓi wannan kaɗan zuka aboki, zata rage maka damuwar nan" kai kurum Abas ya girgiza masa alamar bazai sha ba "Aboki bana son ganinka cikin damuwar nan wai ga manyan babys nan a gari ka tsaya kan wannan yar tatsitsiyar kana ɓatawa kanka lokaci ka shirya a daran yau mu futa club tare, za ka sami wacce zata ɗebe maka kewa ko rumans ku ɗanyi ka rage zafi" Afusace Abas yata shi tsaye yana huci ya nuna Sulaiman "Ki fita sabgata Suleman dole sai nayi rayuwa irin ta ka ne?"danna shiga damuwa saina jefa kaina a bala'i da fishin ubangiji lokacin inada kuruciya ban nemi mata ba, ban sha sigari ba bare yanzu da shekaru na suka haura arba'in, a yanzu fatana da buri na mutuwa a ko yaushe, nifa musulmi ne na yarda da kaddara mai kyau ko mara kyau, domuwar nan da nake ciki jiki da zuciya ne suka kasa sabawa da rashin Aimanah amma na yarda da kaddara daman banada rabon aurenta, inada kur'ani shine yake mantar dani duk wata damuwa, taba sigari ko wata mace tayi kaɗan ta ɗeban kewar Aimanah" fuuu ya fuce daga ɗakin a fusace, Sulaiman taɓe baki yayi ya koma inda Abas yata shi ya kwanta. Murjana tana tsaye gaban closet tana zuba kayanta cikin babbar trolly, da sallama Sumayya ta shigo ɗakin ta zauna gefan bed tana kallon Murjana data zama wata katuwa tayi fari ɗau da alama mai tafara shafawa sabida da ba haka take ba baka ce ba can ba bakinta mai kyau ne "Wai lafiya yaya kika zuba min idanu haka?" "Gani nayi kin zama wata hajiya ga uban fari da kikayi nidai Allah yasa ba blecing kika fara ba" Murjana tayi far da idanu tai juyi ta ce "Ai ina gaya maki kuɗi duniya ne, kinga kuɗin danake kamawa kuwa ai Salim ya kyauta min da ya nunamin wannan harkar yanzuma wani Alhaji zanyiwa rakiya Dubai" "Murjana wai bakiji maganar dana gaya maki ba ran nan, Murja wannan rayuwa bata da tabbas dan Allah kibar wannan harkar ta ɗaukar zunubi" "Nifa inada mijina a hannu kuma shiya nunamin har kar nan ke karshe shiya haɗani da wannan alhajin yace namasa rakiya Dubai" Sumayya tagumi taja tana kallon Murja, Amarya ta shigo ɗakin ba ko sallama tasami gefen Sumayya ta zauna tana aika mata da harara, "Murja ga wannan boka tsito yace a zubawa Alhaji a abinci zai manta dake indai yaci abincin bazai sake tunawa da ke ba sai randa ya ganki" tsalle Murja tayi ta ɗane Amarya tana murna "Sai dake Mama ina alfahari dake uwata maganin kuka na" "Mama yanzu dan Allah kema biyewa Murjana kike keda yakamata ki gaya mata gaskiyya haba dan Allah karuwanci fa kenan kika ɗaurewa Murja kugu tayi a cikin gidanmu" "Gidansu dai, ke kunada gida ne, indai namiji ne gaki nan ga shi nan, badai kince ke kin daina asiri ba karya ne gashi nan ai kin fara gani kina zaune a gidan zaki zama bora, maza Murjana ta shi kije ga Alhajin can ya aiko a ɗauke ki naga irin motar jiya ta paka a kofar gida" Murja ta saɓa jaka a kafaɗarta tasa kai zata fita Amarya ta ce "Yawwa murja nace dan Allah karki manta da abayar nan dana nuna maki irinta babar Salim" "Bakida damuwa Mama zan siyo maki wacce tafi tatan tsada" Sumayya ta kalli Amarya ranta ɓace "Mama maice kuma abaya dan Allah Abba fa yana matukar bakin kokarinsa mai kika nema kika rasa na sittura zaki wane ce a siyo maki Abaya ayau kika gayawa Abba kinason Abaya saiya baki kuɗi kin siya" "Ke! zoki fita daga nan kibar min gida na" "Mama nifa gaskiyya nake faɗa maki" "Sumayya koki fita daga ɗakin nan kona saɓa maki" Sumayya ta fita zuwa ɗakin Ammi suka gaisa sun jima suna hira tana bawa Sumayya hakuri kan auran da Mustapha yayi batareda sanin ta ba ta gaya mata yanda abin yafaru, ta bata shawarar yanda zata zauna da mijinta da kuma abokiyar zamanta Aimanah. Anty Halima sun haɗo kayan lefe na kece raini itada Anty Hasana koda suka kawosa gidan ɗakin Momy suka ajje Anty Hasana bata zauna a gidan ba ta wuce gidan Ana sabida ta gaji sosai, Alhaji Kamal yaga kaya yasa albarka yace akai Momy da Ahmad da Shaheed sukai kayan har zasu tafi Ammi tace "Alhaji Amarya bataga kayan nan ba amata magana" Momy ta leka ta gaya mata tazo taga kaya, ta leko daga bakin kofar sashinta ta tsaya tana karewa akwatinan da takasa kirga yawansu ta taɓe baki ta koma cikin ɗakinta batare da ta ce komai ba, su Momy suka wuce da kayan, Alhaji Kamal yabi Ammi ɗakinta, jiyowa tayi ta kallesa taja ta tsaya tana kallonsa "Madam wai maiya canza minke ne?" "Maizai canza ni kuwa kaine dai naga ka nufi wani waje daban" ajje hular kansa yayi ya zauna saman kujera yana murmushi, "Alhaji daka futa na sameka a ɗakinka bana son rigima kasan dai yau Amarya ce ke dakai" "Sabida itace dani kuma sai akace bazan shiga inda raina yakeso ba, ko wacce acikinku ta sani nakan shiga ɗakin da naso koda ba acan nake ba indai inada magana da ita kema dan rigima kike ji shiyasa kika kasa fahimta" "Au rigima, ni karamar yarinya ce kenan?" " E mana ni a wajena kinfi Raudah yarinta" dariya Ammi tayi ta zauna kusada Alhajin "Bani ruwa na sha" Alhaji Kamal yafaɗa yana kallonta "Nifa Alhaji bazan baka ruwa ba, nama tina banma da shi a ɗakin nan ɗazu nake gayawa Ahmad inya fita ya tawomin da shi" "Babu a story ne?" "E haka Shaheed yace dana ce ya ɗakko yasamin a firij" "Kinga yanda abu yakasance ba zato ba tsammani na tausayawa Aimanah na kuma taya Mustapha murna Allah ya taya sa ruko yabasu zaman lafiya da zuri'a ɗayyiba" "Ameen" Ammi tafaɗa tana kwantar da kai jikin kujerar datake kai "Da sonayi nabasa gidana dake Kabuga ya zauna acan sai kuma Halima take gayamin sun gama magana saman gidan dayake ciki zai gyara ta zauna acan" "Haka nima ɗazu take gayamin hakan yafi amma ya za'ayi ace Aimanah na sama Sumayya na kasa hakan kamar ba tsari" "Haka Allah ya tsara, yace Sai Juma'a zata tare mai kuke shiryawa koba zakuyi taro ba" "Naji Mas'ud ɗazu yana cemin zasuyi Party ranar asabar abar tarewan sai asabar saboda Mustaphan bazai shigo kano da wuriba ranar juma'an jirgin dare zai biyo" "Shikenan na tura masa gudun mawata ta bikin ban samu na masa komai ba" "To yana godiya Allah yakara arziki mai albarka" "Amin" Alhaji Kamal yace bayan ya mike, da sauri Amarya dake laɓe jikin window ta salallaɓa ta koma sashinta tana hucin takaici, Anty Halima ta turawa Musty hotuna da vidion kayan da suka haɗo, Anty Halima ta tsaya kan komai ganin yatafi dai dai itada Ahmad suke komai, tsab aka gyara saman benan inda Aimanah zata zauna Anty Hasana da Anty Ummi sukaje suka gano wajan yayi kyau sosai, Prop yabawa Mah card ɗinsa yace suje da Aimanah ta zaɓi kalar kayan ɗakin datake so, duk yanda sukaso Aimanah taje ta zaɓa ki tayi sai Anty Hasana ce ta zaɓi komai, sukayi komai suka gyara saman inda Aimanah zata zauna yayi kyau sosai, gaba ɗaya Aimanah batada walwala tunda Musty yatafi legos ta kashe wayarta ko yaya Mas'ud yakawo mata wayarsa yace zasuyi magana da Mustapha bata musu kai tsaye zata karɓa daga ya fita zata saka wayar a airplane mode ta ajjeta gefe taci gaba da sha'aninta, daga farko kullum tana cikin kuka da damuwa saida Mah da Daddy suka zauna suka mata nasiha sosai sannan ta hakura ta rungumi kaddararta Mustapha, sau tari takan ɓuya tayi kuka sosai musamman inta tina Abas tanaso tasan halin dayake ciki amma tasan haramcin hakan bata taɓa kwada kiransa a wayaba kamar yanda bai taɓa kiran nataba tun bayan abinda yafaru lambarsa ma bloking ɗinta tayi a wayarta. Sumayya gaba ɗaya ta shiga damuwa musamman sanda taga an kawo kayan Aimanah an jera ta shiga ɗaki tayi kuka sosai har saida idanunta suka kumbura [2/13, 4:44 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na goma sha Takwas* Shaheed ne yaje airport ya ɗakko Musty, suna tafe a hanya sun kusa gadon kaya Musty ya ce "Shaheed bazaka biya dani ta gidan Mah naga Aimanah ba kuwa?" Shaheed da dariya ta kama sa ya rike baki yanaso yayi dariya yana tsoron faɗan Yayan nasu ya ce "Yayanmu ka basar kawai gobe i yanzu fa kuna tare, kuma ma gidan a cike yake da mata ɗazu da Ammi ta aikeni da kyar na samu na shiga banma ga Aimanan ba sai Ruma nabawa sakon ta kai mata" "Au Aimanah ma, bama sakayawa kace Anty" "Yayanmu ai kasan daman Yaya nake ce mata kawai yanzun ma suɓul da baka ne" Musty wayarsa ya zaro yana dannawa Mas'ud yakeson magana da shi tun safe yau yake kiran wayarsa bata shiga, yai sa'a yanzu ta shiga saidai harta gama ring ba'ayi picking call ɗin ba, a kofar gidansa Shaheed ya ajjesa ya shiga, shaheed kuma ya shige gidansu da ma da motar Ammi ya ɗakkosa, Sumayya data sha ado tanajin an buɗe kofa tai sauri ta tashi daga inda take zaune da gudu ta nufisa, Musty buɗe mata hannuwansa yayi ta shiga jikinsa yamaida hannun ya haɗe da jikinta yana zugar kamshin turaranta "Barka da zuwa" Sumayya tafaɗa ahankali tana sake kwantar da kanta a kirjin Mustapha, wani tausayinta ne ya ziyarci zuciyar Mustapha ya tina irin son dayakewa Aimanah indai har haka takeji itama a kansa tabbas ya tausaya mata, ya ɗago kanta yana kallon fuskarta "Kinyi kyau ya kike ya gida fatan na sameki lafiya?" "Lafiya kalau sai kewarka data addabi zuciyata gidan shiru ba motsin kowa" "Gobe iyanzu ai kun zama ku biyu, kinga kin sami abokiyar hira" batace komai ba taja hannunsa zuwa ɗakinsa gefan bed ta masa mazauni tana cire masa takalmin kafarsa "Na haɗa maka ruwa kayi wanka?" kai kurum yaɗaga mata alamar e ta mike zuwa bathroom na ɗakin yabita da kallon tausayawa, ita ta taimaka masa yayi wanka, yai sallah, yayita zuba idanu yaji ance ga abinci yaji batace komai ba shi kuma harga Allah yunwa yakeji, yamike yana kallonta "Bari na shiga wajan Ammi naci abinci inajin yunwa sosai ban samu naci abinci ba yinin yau tun break ina ɗoki zanzo kano" batace masa komai ba yana kallonta ta kwanta saman bed ɗin nasa, shi kuma ya fita daga ɗakin, gidan cike yake da baki yan uwan babansu da suka zo daga sareena harda Mami matar Alhaji Sadik kanin mahaifinsa wacce ya zauna a wajanta a Jordan, da sarsarfa yakarasa wajanta ya rungumeta "Hajiya Mami saukar yaushe ba labari" "Ka daina yina na gidana shiyasa bakama san nazo ba, nima na canza ɗa kafata kafar Shaheed inya tafi ya tafi kenan saidai yazo maku da ziyara, in kuma ya mana irin taka shi kenan" "Hajiya Mami bama zaiyin ba" yafaɗi haka yana sumbatar hannunta "Nayi missing irin sosai ɗin nan, ina Abie na shi bai zoba?" "Bai sami zuwa ba aiki sun masa yawa shiyasa, nayi farin ciki sosai jin wannan labarin buri ya cika Aimah ta zama tamu" "Bari hajiya Mami ansha fama" "Allah yasa albarka" "Amin" yafaɗa tareda shafa kansa irin yaji kunyar nan, inda Ammi ke zauna tana making wasu takardu ya kalla "Barka da dare Ammi" "Barka dai ɗan Mami sai yanzu ka ganni?" dariya Musty yayi kana ya zauna kusada mami "Ammi zan sami abinci" "Matar taka bata dafa maka ba" "Batayi ba wai batajin daɗi" taɓe baki Mami tayi ta tashi ta fita zuwa kicin ɗin gidan, Amarya ce tsaye kan babbar coler abincin kowa ya shigo ita take zuba masa haɗaɗɗiyar fride rice, Mami ta ɗauki ɗaya daga cikin jerin plate ɗin dake jere reras saman babban kitchen wear ta karasa gaban kular tasa babban food spoon zata ɗebo Amarya ta rike spoon ɗin da hannunta tana hararar mami "Lafiya malama kika rigemin hannu?" "Ke bakida ido ne kina kallon kowa yazo ni nake zuba masa amma ke zaki saka hannu ki ɗiba da gadararki" "Sakarmin hannu" Mami tafaɗa a fusace "Anki a sakar maki hannun ko zaki dakeni?" Mami hannunta ɗaya tasa ta murɗewa Amarya hannu har saida yayi kara ta wurga mata plate ɗin a goshi tasa kai zata fita a kichin ɗin, Amarya a fusace tai ta maza duk da zugin da hannunta yake ta shako wuyan Mami tana ihu "Ni zaki daka kinsan dai ni ba sa'arki bace ko" Momy dake tsaye kofar sashinta dayafi kusa da kicin ɗin ita ta jiyo ihun Amarya da sauri ta shiga kicin ɗin dan taga sanda mami ta shiga kicin ɗin shiyasa ma ta tsaya jiran abinda zai biyo baya tasan Mami da Amarya sam basa jituwa, kafin ta shiga Mami ta shako wuyan Amarya tana huci "Naja ni kika zaga, yau zan nuna maki ni ba sa'arki bace" Mami takaiwa Amarya duka a baki nan take bakinta ya fashe nan fa mutane sukayi kicin ɗin ciki harda Ammi dake kokarin janye Mami daga jikin Amarya da aka fasawa baki, Musty shi dariya ma abin yabasa ya fice daga gidan bayan ya karɓi car key ɗin Ammi a hannun Shaheed, wani lafiyayyan wajan cin abinci yaje ya cika cikinsa daga nan ya wuce shagon aski, agida kuwa cacar baki ake sosai tsakanin Mami da Amarya har saidai Alhaji Kamal ya tsawatar sannan Amarya ta wuce ɗakinta tana kuka yayinda Mami ta wuce ɗakin Ammi tana haɗa kayanta, Ammi dake tsaye gaban Mami cikeda damuwa ta ce "Yanzu dan Allah Hajiya Binta in kika tafi a ina zaki kwana keba yan uwa ne dake a kano ba bare nace kyaje can ki kwana, dan Allah kiyi hakuri ki manta da Amarya kin rigada kinsan halinta haka ta mana rashin mutuncin nan a bikin Halima" "Kiyi hakuri Saudat bazan kwana gidan nan ba, inna zauna komai zai iya faruwa gara ko hotal ne na kama gobe ma haɗu a event" "Kinsan Allah ba inda zaki, bari kiga na kira Alhaji" da kyar Alhaji Kamal da Ammi suka lallaɓa Mami ta zauna a gidan, daga ɗakin Ammi Alhaji Kamal ɗakin Amarya ya shiga ya mata tatas yace in fitina zata tada masa a gida ta fita in angama taro ta dawo, Amarya tana kuka ta kira Boka tsito ta gaya masa yanda sukayi da Alhaji Kamal yace mata ta tawo wajansa su kwana suna aiki shi kuma zai mata abinda ko mai zatayi a gidan Alhaji Kamal bazai sake ce mata komai ba, nan take ta ɗauki kayanta kala biyu tabar gidan batare da kowa ya san bata gidan ba, kai tsaye tasha ta nufa ta hau motar da zata sadata da garin da Boka tsito yake, kwance ta samesa a yar bukkarsa saman wata yaloluwar katifa, kusa da shi ta zauna fuskarta fal damuwa "Doguwa mai dogon zunubi nifa bana son ganin fuskar nan taki a damuwa in kina damuwar nan ai bazaki bani nishaɗi ba ki saki jikinki mu more daran nan inna lashi zazzakar zumar nan taki zan maki wani aiki da Alhaji kamal zai manta da kowa ke kawai zai rinka gani" "Tsito ni yanzu ba wannan ne yadame ni ba yaya za'ayi nima nasamu na haifi ɗa namiji a gidan Alhaji Kamal" wata dariya boka Tsito yayi tareda fito kana ya ce "Mai dogon zunubi, bazaki kara haihuwa ba ke a zuri'arki ma kaf cikin yaranki ba wanda zai haifi ɗa namiji Murjana ma na hango batada rabon haihuwa Sumayya ce dai keda rabo itama ba nan kusa ba" matsowa kusada ita boka yayi yafara shafa jikinta da kamar bazata biye masa ba amma daga baya ta bada kai bori ya hau, sassafe kuwa saiga kiran Alhaji Kamal yana tambayar ina taje gidan duk yamasa duhu ta daure ta dawo, tace zata dawo amma ba ranar ba sai an gama biki kamar yanda ya bukata, gaba ɗaya ya burkice mata kan lalle saita dawo, kallon boka tayi tana jinjina masa "Na kara yarda da aikinka bokana" Hhhhhhh "Indai zaki bani jikinki doguwa ba abinda bazan maki ba, ina mu'a mala da mata daban daban amma keta musamman ce, yau bazanga kowa ba muna nan tare, sannan sharaɗin aikinmu bazakiyi wankan tsarki ba koda kunyi mu'amala da Alhaji Kamal sannan baza kina sallar asuba da la'asar ba sannan duk ranar Juma'a nan zaki rinka kwana ko ni nasa aljani dundurusu ya kawoni gidan naki na kwana acan" "Boka wannan abunfa yayi yawa, nifa ba gamsar dani kake ba wannan aba taka kamar ta jariri bata kaimin inda nake bukata a sauya wani salon na gaji da wannan" "Dakata doguwa karki sake faɗan irin wannan kinsan adadin matan da suke son su sami damar da kika samu kuwa, kimin shuru kika sake faɗar haka saina rushe komai zaman duniyarki saiya girgiza ki bini a yanda nake, kimin abinda duk nakeso matso nan" boka ya kirata yana zare mata manyan idanunsa, jiki na rawa ta karasa gabansa. Murjana na kwance jikin Alhaji Jameel tana wasa da gemunsa shi kuma yana waya da alama da matarsa yake waya, Murja da taji yana sumbatar matarsa ta cikin waya tai saurin mikewa zata bar wajan ya ruko ta yasake haɗata da jikinsa sosai ganin tana kokarin kwacewa yasa yayiwa matar tasa sallama ya ajje wayar yana kallon Murjana "Baby ina zaki ki barni ne" "Ya zaka sumbaci wata katuwa a gabana" "Murja ke yarinya ce, kinada kyau, maiya kawo ki cikin wannan kazamar harkar dazaki yadda da munyi aure" "Aure kuma My yaya zanyi aure yanzu ban gama more kuruciyata ba" "Murja magana ta gaskiyya zan gaya maki ni harga Allah bason raina nake wannan harkar ba mata tace tajamin ni ɗan kasuwa ne nine yau wannan kasa gobe nine waccan kasar nayi nayi da matata akan ta rinka bina ko ina zani amma taki sabida tana koyarwa inta cika yawo zata sami matsala da makaranta na gaya mata zan dinga biyanta duk wata fiyeda yanda ake bata albashi amma taki, nace mata zanyi aure ta tada hankalinta ki yarda na aure ki bazan ajjeki a nageria ba zan ajje ki duk kasar da kike so a faɗin duniyar nan inyaso duk inda zani muna tare" "Alhaji nifa bazanyi aure yanzu ba in aure kake so kanemi wata" Murja tana gama faɗar haka ta kwanta saman bed, Alhaji Jameel ya mike ya shiga wanka tana kallonsa ya fito ya gama shiryawa ya kalleta "Zan fita yau baza kimin rakiya ba?" "Ba inda zani jiya ka hanani barcin sannan yanzu kace nazo na rakaka, daga mundawo kuma kace zaka ɗora daga inda ka tsaya kaje kawai kanka dawo na huce gajiya saimu raba taka gajiyar" futa Alhaji Jameel yayi yana kallon Murjana yana lasar leɓe, Murja barci ne ya ɗebe ta can cikin barci taji ana loking ɗin kofa, sakkowa tayi daga gadon tana mika ta buɗe kofar kyakkyawar matashiyar mata ce ta shigo ɗakin kallo ɗaya Murja tayi mata ta gano yar nageria ce itama "Sannu, kece Murja ko?" Murja kai kurum ta ɗaga ta kasa magana ganin matar na kokarin cire kayanta, Murja jikinta ne yaɗau karkarwa ganin matar ta nufota gadan gadan gaba ɗaya ta gama cire kayan jikinta, "Kinga saki jikinki Salim ne ya bani adress ɗinki tare mukazo kasar nan da mijina ya hanani sakewa ni kuma na riga da na saba ma'a mala da mata duk banajin daɗi dana gayawa Salim yace nazo zaki ɗan ragen zafi "Murja innalillahi kawai take ja a fili tana yin baya harta kai kofar bathroom da sauri ta faɗa ganin matar tana biyota tai saurin rufe kofar, daɓar ta zauna kasan tiles na banɗakin gabanta na dukan uku uku, yau taga masifar datafi karfinta ita kanta baima taɓa bata akwai wata ma'a mala tsakinta da mace ba, kuka take sosai tana jiyo matar tana kwaɗa mata kira akan ta taimaka ta buɗe dan Allah ta rage zafi, tajima tana bugawa amma taki buɗewa can taji shuru tsawon lokaci azatonta ta tafi ta buɗe ta fito kwance ta sameta male male a gado tana biyawa kanta bukata, jikin Murja rawa yake sosai ta zauna nan tsakiyar falo tana kuka wiwi tana kallo matar ta gama abinda take ta shiga banɗaki ta gyara jikinta ta fito ta shirya ta fita, bata jima da fita ba kiran Salim ya shigo wayarta jiki na rawa ta ɗaga "Salim ka cuce ni Allah ya isa tsakani na dakai shine ka turomin wata yar iskar mata" wata dariya Salim yayi kana ya ce "Naga fa kuɗi kike so shine na turo maki ita wannan matar da kinsan wacece da baki wulakanta taba minti nawa ne anyi an gama kin bani kunya ba kuɗima kike so ba, ni a gabanta ma nake biyawa mijinta bukatarsa ya bani Money na tafi ita ta haɗani da mijinta wani bin in ina bukatar kuɗi Daddy na yaki bani ita nake nema abokiyata ce sosai" "Salim" Murjana ta kira sunansa da karfi "Yane, kinga yarinya nifa taimakonki nake son yi so nake na maidaki babbar yarinya babban kai" "Salim Allah ya isa tsakani na dakai, nayi dana sanin saninka a rayuwata" katse kiran tayi taci gaba da kuka wiwiwi nan Alhaji Jameel ya tarar da ita ya rinka lallashinta kan tayi shuru amma taki daya takurata ma ce masa tayi "Dan Allah taimakarni ka sama min jirgin da zai maidani gida gobe yau naga abinda ya girmi kakata" duk yanda yaso tayi shuru ki tayi dole yayi abinda tace washe gari ya tattarata yasa ta a jirgin da zaizo nageria Murja ta sauka gida a firgice, bata sami Amarya ba gidan anata shagali haka ta shiga ɗakin ta kwanta tanajinta kamar mai zazzaɓi. [2/13, 4:44 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na goma sha Tara* Ranar asabar biki ata tashi dashi sosai a gidan Alhaji Kamal da Prop Faruk, tun bayan sallar azahar ahalin suka fara shirye shiryan tafiya wajan party wanda za'a fara karfe huɗu na yamma, Prop yasa Anty Hasana ta kawi masa Aimanah har ɗakinsa ta fita ta basu waje "Ummu Aimanah kiyi hakuri ki ɗauki kaddarar yanda auranki ya kasance bazance ina farin ciki da auran nan ba, kamar yanda bazance ina bakin ciki ba, ina maki fatan alkhairi tareda fatan zaman lafiya da zuri'a ɗayyiba, kibi mijinki sau da kafa kiyi masa biyayya aljannarsa tana karkafim kafarsa, kirga wai ko bakya sonsa ko baki shi kika so aura ba kice zaki munana masa Allah zai kama ki da laifin saɓawa miji, Aimanah kibi mijinki ki masa biyayya kamar yanda kikaga mahaifiyarki nayi, kina dai ganin yanda muke da ita a gidan nan, Aimanah karki ɗauki zugar kowa akan kiki Mustapha, mun riga da mun sani kinason Mustapha a baya sai dai da hausawa sukace so tsuntune, ina maki fatan alkhairi da zaman lafiya da kaunar juna tsakaninki da mijinki, daga wajan party nacewa Hasana a wuce dake gidan Alhaji Kamal daga nan mijinki ya ɗaukeki zuwa gidanku" Aimanah tunda Daddy yafara magana kuka take sosai, har gama ba abinda tace, tanaji ya kira Hasana tazo Anty Hasana ta mikar da Aimanah tsaye da sauri Aimanah ta kwace daga hannun Hasana da gudu taje ta rungume Daddy tana cigaba da kuka "Daddy bazan iya tafiya na barka ba" Aimanah ta faɗa cikin kuka "Aimanah aiba nisa kikayi ba ko yauahe muna tare har gidan naki zanna zuwa, maza bi Hasana kije ki shiri Allah yabada sa'a yakawo zuri'a ɗayyiba" Anty Hasana ta amsa da "Amin" taja hannun Aimanah zuwa ɗakin Mah inda mai kwalliya take jiranta sai da tayi sallar la'asar sannan aka fara mata kwalliyar gidan yayi shuru kowa ya wuce wajan party lokacin da aka gama mata kwalliyan ta saka Jan swees lace mai kwalliya ta ɗaura mata head shima ja ta saka mata nett a kafaɗanta, Anty Hasana itace karshan tafiya a gidan ta barta daga ita sai Mah da yan tsirarun kawayn Mah da bazasu wajan partyn ba, Yaya Mas'ud ne yazo ya fita da ita har waje bayan mota ya buɗe mata ta shiga idanunta a rufe da sauri ta buɗe idanunun tana kallon gidan nasu" hannu taji saman nata da sauri ta kalli gefanta inda take a zaune, Mustapha ne zaune kusada ita, sam ita batama san yana cikin motar ba, hannunta daya sha lalle yake karewa kallo ya ɗago hannun ya sumbata yana kallon fuskarta "Alhamdulillah nagodewa Allah daya mallakamin ke" matsowa yayi sosai kusada ita ya ɗora kanta saman kafaɗarsa, ahankali yake sauke ajjiyar zuciya kamar wanda yai tseran gudu, waje yayi waje taro ne sosai akayi na manya kowa ka gani yana cikin nishaɗi anci ansha sai abinda kaga dama zaka je da kanka ka ɗibi son ranka, ansha rawa sosai musamman Rumaisa da Yaya Ma'aruf sai gafda mangariba aka tashi, Anty Hasana ce ta ɗauketa a motarta zuwa gidan Alhaji Kamal kamar yanda Daddy yace, anan falon Alhaji Aimanah tayi sallar mangariba, yakira Anty Hasana "Hasana ina fatan ku gama dodon zuwa ganin ɗakin amaryar?" Alhaji mun gama tun tuni kowa yama watse" "To masha Allah sannunku da hidima Allah ya bar zumunchi yanzu da kaina zan kai Aimanah har ɗakinta" Alhaji sosai yayiwa Aimanah nasiha kwatankwacin ta Daddynta sannan yasa ta a gaba har gidan Mustapha ta kofar dake cikin gidansa suka bi suka shiga gidan, Abba gaba ɗaya ya haɗa Mustapha da Sumayya da Aimanah "Gaba ɗayanku ƴaƴana ne ku, dan haka ina umartarku daku zauna lafiya kuyi kishi islamiyya irin na gidan Annabinmu Muhammad S A W kuyi zama na amana banda gaba ko faɗa na rokeku ku zauna lafiya, ke Sumayya kece babba ga Aimanah nan ki zauna da ita lafiya kija girmanki, sannan ke Aimanah ga Sumayya nan ki bata girmanta ki mata biyayya kinga kece kasa da ita, Mustapha ga matanka nan na umarceka da kayi adalci a tsakaninsu" sosai Abba ya masu nasiha kafin daga karshe ya umarci Aimanah kan ta tashi ya rakata sama, har bedroom ɗinta Abba ya kaita sanda zata shiga ya ce ta karanta "A'u zu bi kalimatillahil tamatan min sharri ma kalak" sau uku saida tayi kana suka shiga ɗakin da bisimilla ta zauna gefan gado yana daga tsaye ya kara yi mata nasiha da fatan alkhairi yace taje tayi alwala tayi sallah raka'a biyu ta godewa Allah sannan ta rokesa zaman lafiya da zuri'a ɗayyiba, saida ta tada sallar sannan ya fita daga ɗakin kasa ya sakko ya tadda Mustapha zaune shi kaɗai Sumayya bata wajan, Musty yabi bayan Abba yana masa godiya "Ka koma daga nan Al'Mustapha Allah yamaka albarka ya albarkaci auranku yasa nan da wata tara nazo naga babys" Musty ya shafa kansa yana mirmushi "Au bazaka amsa ba" Abba yafaɗa yana kallon Mustapha, Musty kasa yayi da kai yana shafa kansa da hannu ya ce "Abba addu'ar ce tayi nauyi ai" "Ok toni bari na ce Amin" murmushi Musty yayi, Abba yai kasa da murya kamar mai raɗa "Maza maza koma ciki ka rarrashi uwar gida kaje ga Amarya" da sauri Musty ya juya yana dariyar maganar Abban nasa, ɗakin Sumayya ya shiga ya sameta kwance saman bed ɗinta tana kuka, daga bakin kofar ya tsaya bai shiga cikin ɗakin ba "Amma dai nace ki daina kikan nan ko, ya mukayi dake ɗazu?" mikewa zaune tayi tana share hawayan fuskarya cikin kukan ta ce "Nayi shuru fa" ajje mata ɗaya daga cikin ledojin hannunsa yayi waɗanda ya ɗakkoau a motar sa sanda ya raka daddy, ya matso ya sumbaci kuncinta yai mata sai da safe, wajan daya sumbata tasa hannu da shafa ta sumbaci hannun nata, Musty kai tsaye ɗakinsa ya shiga yai wanka yasa jallabiya marun ya fesa turare ya fito daga ɗakin kofar ɗakin sumayya ya koma ya rufe da makulli ya zare key ɗin yayi sama yasan akwai wani key ɗin a cikin ɗakin, sanda ya shiga ɗakin Aimanah na zaune saman dadduma ta ɗaga hannu tana addu'a, shima hannun ya ɗaga kamar yanda tayi saida ta ahafa sannan shima ya shafa haɗeta faɗin "Amin" kasa Aimanah tayi da idanunta, zama yayi a gabanta ya ɗaga mayafinta yaga kuka take sosai, jikinsa ne yai wani irin sanyi ganin irin kukan da take wanda kafin shugowarsa ba kukan take ba, ta tabbata Aimanah da gaske bata sonsa, jingina yayi da gado ya kwantar da kansa saman gadon fuskarsa na kallon p o p silin na ɗaki lokaci ɗaya hawaye suka wanke masa fuskarsa "Reina da gaske kin daina sona bakya farin ciki da auranmu ko?"nayi nadamar kin zuwa wajan ɗaurin auran nan da banyi ba, inama zan iya dawo da baya da ban bari Yaya Mansur ya ɗaura mana aure ba, nasan da tini najima a kabarina" da sauri Aimanah ta yaye mayafinta tana kallonsa "Ni nace maka na daina sonka, mu manta da wata soyayya anriga da an ɗaura min aure da kai ba yanda zanyi" wani sanyi yaji a zuciyarsa hakan yabasa karfin gwiwar umartarta kan ta tashi suyi sallah suyi godiya ga ubangijinmu batayi masa musu ba ta mike ya jasu sallah raka'a biyu sukayi ya jima yana addu'a kafin daga karshe suka shafa tare, da kansa ya fita zuwa kicin ya samo plate ya juyo naman daya shigo da shi a hankali yake bata tana ci bata wani ci dayawa ba ta kurɓi lemun exotic ta tashi ta jima zaune gefan gado tana kallonsa ya gyara ko ina ya fita da sauran naman ya ɗebe komai yakai kicin tana jin motsin shigowarsa ta kwanta tana barcin karya , ya cire jallabiyan jikinsa ya rage daga shi sai gajeran wando da singlate ya zauna wayarsa tayi kara alamar kira ya shigo "Anty Hasana" ya furta a fili sanda yaga sunanta na yawo saman madubin wayar "Assalamu alaikum" Musty yafaɗa a hankali "Yawwa nace Musty dan Allah kabi yarinyar nan a hankali, kaga dai ita ba..." da sauri Ammi ta kwace wayar daga hannun Anty Hasana "Nashiga uku ni Saudatu, Hasana maine kukeyi haka, kefa bakida girma saina jikinki, so kike yaron nan ya rainaki ko" Anty Hasana cikeda damuwa ta kalli Ammi "Wallahi Yaya Saudat gaba ɗaya na kasa samun nutsuwa tausayin Aimanah nakeji kinga kuwa irin kallon da Musty yakewa Aimanah ɗazu ni kawai nasan mai na gani cikin idanunsa" Mami dake kwance saman bed ɗin Ammi dariya takewa Anty Hasana "Ke mai ƴa ko to wallahi ki kama girmanki" Mami tafaɗi haka tana dariya, acanma Mustapha dariya yayi "Hmm Anty Hasana ikon Allah" yafaɗa sanda ya zauna a gefan gadon ya kalli Aimanah da idanunta ke rufe amma suna motsawa ita nan bata yarda ba barci take, "Alhamdulillah" yaketa jerawa "Aimaah tashi ki rage kayan jikinki" sake takurewa tayi waje ɗaya, tayi shuru batace komaiba "Nariga da nasan ba barci keke ba ki tashi kafin na cire maki da kaina" da sauri ta tashi zaune yanda ta tashinne yabasa dariya hakan yasa ya murmusa "To sakko ki canza kaya, kona canza maki da kaina" "Nifa banda wasu kayan anan duk suna gidan Mahh" "Wanda su Anty Hasana suka kawo jiya fa" mikewa yayi ya buɗe wardrove ya ɗakko mata ɗaya daga cikin jerin ringunan barcin dake ciki "Karɓi wannan kisa" "Sanyi fa ake Man kace nasa wannan" tafaɗa tana juya rigar a hannunta "Ok tayi kauri da yawa ko, to bari na canzo maki wata" "Kifita na canza rigan to" gyara zama tayi saman bed ɗin yana kallonta "Ni ba inda zan fita ki canza kawai inace mum riga mun zama ɗaya kunyar me kuma zakiyi" turo baki tayi gaba alamar shagwaɓa "To gyara na sauka na shiga bathroom na canza" gyara kafarsa tayi ya mata hanyar da zata sauka daga gadon, tana matsowa kusada shi yai saurin janyota ta faɗo jikinsa, hannun yasa saman gwon ɗin tata yaja zif kasa "A'a dan Allah ka bari Kalbie" "Kalbie" Musty ya maimaita sunan a hankali "No Aimah Hayatie Kalbie duk bana son jinsu a gidan nan kibar abinki a gidan Mah bana son jin word ɗin nan" Musty yafaɗa a fusace, karasa zuge zif ɗin yayi kana ya ɗora hannunsa saman riganta ta ciki yana kokarin ɓallata, gaba ɗaya Aimanah ruɗewa tayi ta rike hannunsa kam kamar zatayi kuka "Yayanmu Please dan Allah" "Ina yayan naku anan" ya raɗa mata a kunne yana cigaba da ɓalle rigan, gaba ɗaya ta makalkalesa sanda taji ya gama ɓalle maɓallin rigan tata, "Ya Musty banaso dan Allah ka bari" ɗago da fuskarta yayi yana kallon cikin idanunta, ita kuma tayi kasa da kanta "Nabar me?"nabari karna canza maki kayan ki kwanta da wannan, nasan fa bakya kwanciya da kaya masu nauyi kinsan na san wannan ba tun yau ba,ki saki jikinki dani gobe da safe so nake kimin wanka da kanki ki wanke ni tas" sake bawa Aimanah kunya yayi hakan yasa tai kasa da kanta sake ɗagowa da kan nata yayi ya haɗe bakinsu waje guda🙈 Abubuwa masu nauyi da girma sun faru a wannan dare mai ɗimbin tarihi a wajan Aimanah da Mustapha, Musty ya maida Aimanah cikakkiyar mace bayan yasha kuka cizo da yakushi🤣daga karshe dai ya ɓige da lallashi da ban bakin kalamai masu ɗimi, da kansa ya wanke ta tas bayan yasa ta gasa jikinta cikin ruwan zafi, yabata riga da wando masu kauri na barci tasa a jikinsa tai barci, godiya yake tayiwa Allah a zuciyarsa da wannan kyauta da yamasa ba zato ba tsammani, yazama dole ya godewa Ya Mansur bandama dare yayi da yanzu zai kira sa shi saima yanzu ya tina bai gansa a wajan party ba, agogo ya kalla yaga karfe goma da kwata na dare, kwanciya ya gyarawa Aimanah a jikinsa ya sake rungumeta a jikinsa yana jin wani sabon sonta da kaunarta na daɗa shigarsa Sumayya kusan kwanan zaune tayi tunda asirin da sukayiwa Al'mustapha ya karye ban sake bin ta kanta ba a shimfiɗa sai jiya, hakan yasa yau take jinta duk ba daɗi bazata taɓa manta jiya ba a rayuwarta sabida rana ce da ta kasance da Mustapha ta kwana a jikinsa tayi barci mai daɗi, hawayan idanunta ta goge ta ɗauki wayarta ta shiga youtube tana kallo ko zai mantar da ita damuwarta, Aimanah tun barcin farko da tayi ta farka barci bai sake ganin idanunta ba, juyi kawai take wani bin har tashi zaune take taga yanda Musty ke barci hankalinsa kwance ya wani dungule waje ɗaya yana fitar da numfashi a hankali kai daga gani kasan yanajin daɗin barcin nasa sosai, sake shiga bathroom tayi ta haɗa ruwa mai zafi ta shiga ciki wani tsananin zugin azaba takeji a kasanta, ta jima sosai cikin ruwa sannan ta fito tana tafiya a hankali kamar mai koyon tafiya tsayawa taji jikin kofar bathroom ɗin tana ɗan hutawa, dai dai sannan Musty ya farka da sauri yata shi zaune ganin Aimanah tsaye "Yadai reina maiya faru" idanunta suka kawo kwalla dai dai sanda ya karaso inda take tsayan ya kama hannunta ya zaunar da ita gefan bed "Kai ba barcinka kake ba ka barni da azaba" kama baki yayi yana yar dariya kaɗan kaɗan "Au wai wajan bai dana zafin ba, ko sakewa zanyi kila ya daina" da sauri ta karasa hayewa gadon tayi ta juya masa baya, balanket taja ta lulleɓe duka jikinta har kanta, Murmusawa Musty yayi kana ya hau gadon shima ya kwanta nesa kaɗan da ita,da asuba bayan yadawo daga masallaci a kan dadduma ya tarar da ita, gaidasa tayi ta koma ta kwanta bayan ta gama azkhair na safiya, Musty zanin gadon daya cire jiya daga kan gadon wanda yaɓaci da jini ya ɗauka ya sakko kasa da shi ya zagaya can bayan gidan ya wanke ya shanya kana yadawo, ɗakin Sumayya ya shiga ya tarar tana gyangyaɗi saman dadduma "Barka da safiya Yayanmu" "Barka dai Sumy fatan kin tashi lafiya?" "Lafiya kalau" shuru ya biyo baya kana ya mike ya fita yana faɗa mata ta kwanta ta huta, sanda ya koma saman tini Aimanah tayi barci, shima kwanciyar yayi, harya mike zai fita gidan Ammi sai kuma ya koma ya kwanta bayan ya kalli agogo yaga har sannan bakwai na safe batayi ba,barci yakoma shima Aimanah ta riga sa tashi wanka tayi ta gasa jikinta ta dawo ta shirya cikin Atamfa ɗinkin riga da siket ta kafa ɗaurin ɗan kali kalar na yammatan wannan zamanin ta ɗauki wayarta tana chat, sai wajan tara da rabi Musty yatashi a barci idanunsa kan Aimanah suka sauka ya bi kyakkyawar fiskarta da kallo tasha kwalliya fuskar nan tayi kyau sosai, batasan yatashi ba hakan yasa lokacin daya saka bakinsa saman kunnanta yana mata raɗa ta firgita tai wurgi da wayarta saman tiles haɗe da sakin kara "Matsoraciya nine fa" "Kai Yayanmu Allah ka tsorata ni" "Nifa karki sake kirana da wani Yayanku malama kisamin suna mai daɗi irin na masoya" cuno baki tayi gaba tana harararsa ta sunkuya ta ɗauki wayarta, rau rau tayi da idanunta tana kallon wayar ta fashe da kuka, Musty ya leko ya kalli wayar yaga yanda ta fashe, taɓe baki yayi yana kallon yanda Aimanan take kuka "Abas ya fashe ko?" yafaɗa yana haɗe rai, kallonsa tayi batace komai ba zuciyarta taji tana mata zafi shi kenan ta rasa wayar nan ita kaɗai ta rage mata wacce inta kalli wayar takan tina da Abas, ta tina lokacin daya bata wayar ta sake rushewa da kuka, mikewa Musty yayi ya shiga wanka, yana fitowa ya fice daga ɗakin bai kalli ko inda take ba....✍🏻 *Alhamdulillah daga wannan page ɗin bazan sake posting a ko wanne group ba sai group ɗin Aimanah real fans group 2 dan haka wanda yakeson cigaba da karantawa zai iya min magan ta wannan lambar 07039793439 zanyi adding nashi a group ɗin karku manta free book ne naku kawai comment* [2/13, 4:44 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na Ashirin* Aimanah ta sake rushewa da kuka ta kwanta saman gado ganin ya fita bai kulata ba, tasha kukanta ta gode Allah har sanda taji cikinta yafara kiran ciroma futowa tayi falonta ta tsaya tana karewa ko ina kallo, kofar datake kallonta ta shiga inda take zaton nan ne kicin, ta kuwa gano dai dai, tsaye tayi tana karewa kicin ɗin kallo, komai yaji alhamdulillah babu ce kawai babu a kicin ɗin share hawaye tayi tana godewa Allah, tareda yiwa Daddy da yayunta addu'a, dubawa ta hau yi ko zata sami wani abin da zata sarrafa tasawa cikinta, gaba ɗaya ta gama dubawa ba komai na nau'in abinci a kicin ɗin hakan yasa ta fito falon ta zauna. Mustapha dake tsaye a ɗakinsa yagama shiryawa cikin koriyar shadda sai sheki take da walkiyya mai ɗaukar idanu, yana saka hula yajiyo sallama daga falo kamar ma muryar Aimanah yaji kamar bazai fito ba sai kuma ya leko ya tsaya daga bakin kofa, Rumana ce tsaye itada Surayya dake rikeda basket cikeda kuloli kala kala, Rumana na rikeda manyan flask tea guda biyu karasa fitowa yayi daga ɗakin nasa yana kallon yaran da suka risina suna gaida sa, ya kalli Rumana "Ke ce kika zo sai wani kwaɗa mana sallama kike da wata muryarki irinta Aimah" "Lah Yayanmu kaima kaji?" kowa wai haka yake cewa muryarmu iri ɗaya" "Hakane ni nazaci ma itace" Musty ya karɓi kayan hannun su yace "Kuje to mungode ayiwa Ammi godiya, anjima kwa dawo yanzun Aimah barci take" "Yayanmu ba Ammi bace tabayar Mami ce ta haɗa da kanta" "To amata godiya zan shigo anjima" suka juya suka fita Rumana na dariya ta kalli Sumayya "Mai kika fahimta da Yayanmu ya hanamu hawa sama wai Aimanan tana barci" dariya Surayya tayi ta rike baki tana waigen kofar da suka fito, "Yagama kashe arna shiyasa bayaso muje mu ganta" "Wayaga idon yaya Aimanah yau anji maza" dariya sukayi gaba ɗaya, Al'Mustapha sama ya haye, Aimanah tai saurin mikewa ta taresa ta karɓi kayan hannunsa ta ajje saman center teble ɗin dake cikin falon, juyawa yayi zai fita da sauri ta rukosa tareda rungumesa ta baya tasa hannunta ta zagayesa "Hubbi kayi hakuri ni fa ba shine ya saimin wayar nan ba yah Mus'ab ne" juyowa yayi yana mata murmushi ya sumbaci leɓɓanta tareda haɗeta da jikinsa yana sakin numfashi a hankali "Naji inma shiya sai maki oho" yafaɗa yana lakace mata hanci, tare sukayi break cikeda so da kauna, bayan sun gama tare suka shiga kicin suka wanke abubuwan da suka ɓata, yana wankewa tana ɗaurayewa, tsokanarta yake tana dariya cikeda shaukin so da kauna, hannunta ya rike har zuwa ɗaki bayan sun gama gyara ko ina gefan gado ya zaunar da ita, "Kiyi barci ki huta Reina zan fita, bama da komai na kayan abinci a saman nan zan aiko Shaheed ya kawo komai, sannan zanje gidan Mah, dafe kansa yayi "Wayyo ni yau ko da wanne ido zan kalli Mah" gaban madubi ya karasa ya ɗauki fashashahiyar wayar Aimanah yasa a aljihu yadawo kusa da Aimanah ya sumbace ta yayi gaba yana mata bye bye, Aimanah ta saka kanta kan filo ta kwanta tana share hawaye, shikenan ya rabata da wayar Hajiya Hafsatu ta ajjewa Alhaji Abubakar wada lemu da ruwa a gabansa ta jiyo zata bar wajan, hannunta ya ruke ta juyo ranta ɓace tana kallon mijin nata "Hajiya tunda abin nan yafaru kinbi kinsawa zuciyarki damuwa kin fita sabgata kamar wanda yai wani gundumememan zunubi" Hajiyar Abas ta goge hawayen da suka kwaranyo a fuskarta ta zauna kusada Alhaji tana cigaba da goge hawayan fuskarta "Alhaji wacce irin zuciya ce da kai? baka tausayin ɗanka, yarannan Abas shekarunsa arba'in da ɗaya kenan adauniya idan ban manta ba, a wannan shekarun nasa bai taɓa kallon wata ƴa mace ba kallo irin naso sai Aimanah, sanda yazo mana da zancan nan munyu farin ciki nida kai muka sanya albarka amma saboda can wani dalili naka ka rusayawa yaron nan duka farin cikinsa, rabon dana ga Abas yayi kuka shekaru sha bakwai kenan, sai rana irin ta yau yayi kukan dabai taɓa yin irin saba a rayuwarsa, amma ko ajikinka yau satin Abas ɗaya rabonsa da gidan nan amma abin bai dameka ba, cikin kwanakin nan bance ka kira wayarsa ba bare kaji a wanne hali yake ciki, kasani haifar Abas dakayi bashi zai hana Allah yakama da laifi ba idan ka ɓata masa, shima mutum ne kamar kowa, kai waye ya hanaka auran wacce kaso mahaiyarka ita ta tsaya maka kai da fata alokacin da gidanmu suka so hana auranmu" Hmmm Alhaji Abubakar Wada Iliyas ya sauke ajjiyar zuciya tareda share hawayen da suka zubo masa "Nayi kuskure tabbas Hafsat nayi nadama, ba yanda Faruok baiyi daniba akan mu tsaya mu sasanta mu fahimci juna amma naki na kafe, kaicona kaicona tabbas ban kyautawa Abas ba, hajiya kiramin Abas yadawo ayau ɗin nan nakoma na nema masa auran Aimanah" "Anriga da an ɗaurawa Aimanah aure da wani ɗan uwanta tsohon saurayinta kamar yanda labari yazo mana nida Abas, sai dai ka nemi yafiyar mahaifin Aimanah ku sasanta, kamanta da duk wata gaba, sannan kasan yanda zakayi da Abbas" Alhaji Wada ɗora kansa yayi saman kujera ya runtse idanunsa da hawayan tausayin Abas suka cika masa idanu "Hajiya kiri min Abbas a wayarki" sau biyu hajiya na kiran wayar Abas tana shiga amma ba'ayi picking ba, ana uku data kirane Sulaiman ya ɗaga shiya shaida mata Abas yana hospital ba lafiya jininsa ya hau, hankalin hajiya yatashi sosai nan ta tubure mota zatabi zuwa garin dayake da kyar Alhaji ya lallasheta kan tabari sai gobe subi jirgin safe. Amarya tashiga ɗakinta bako sallama turus taja ta tsaya tana kallon Murjana dake kwance saman gado kamar mara lafiya cikeda firgici ta karasa gaban gadon tana taɓa jikin Murjana "Murja mai zan gani duka kwananki nawa da tafiya dubai ɗin nan kikace sati biyu zakuyi da Alhajin" Murjana ta fashe da kuka tana bawa Amarya labarin abinda tagani yatashi hankalinta ya hanata barci, tsaki Amarya taja ta zauna gefan gado tana hararar Murjana "Yanzu sabida ɗan wannan abun kika baro Dubai ɗin, kai Murja kinyi asara wallahi, tur maye a cikin wannan ɗan abu na lokaci ai koni na samu yi zanyi badai za'a bani kuɗi ba, kai Allah wadaranki Murja" "Mama tayaya zan iya aikata wannan babban zunubin, nayi nadamar biyewa Salim danayi ma harya sani aikata zina yake kuma so ya sake jefani a wata masifar Mama na tuba na daina harka da maza aure zanyi" "Murja aure kuma yanzu? maiye a cikin auran banda tarin damuwa kina dai kallon halin da yar uwarki ke ciki ai garama ki ci duniyarki da tsinke kiga duniya ki wataya, nima yau na haɗu da wata hajiya a wajan boka tamin tallan harkarsu ina ganin ciki zan faɗa kawai nima nasami kuɗi na daina dogaro da abinda Alhaji zai ban daman ai duk gidan nan nice banda abin yi, Ammi na koyarwa a sa'adatu rimi Momy principal ɗin makarantar sakandire ce, ni ce ba cas ba ass to nima na sami abin yi in auran zakiyi sai kije kiyi kyaji da abinda kika tarar a gidan mijin" "Mama karki min baki mana, ke kullum bakinki baya faɗar alkhairi ne, bantaɓa ji haka kurum kin samin albarka ba sai dai in kuɗi na kawo maki ke kawai abaki ki kawai boka kika sani, kina kallo tareda Surayya da Shaheed muka kammala scoundry school a year ɗin Ammi gashi nan tanata fafutukar samawa ɗanta gurbin karatu a malesia Surayya tuni ta fara poly amma ni karatuna baya gabanki kiwai inje inbawa karti kaina su bani kuɗi na kawo maki, ko sau ɗaya baki taɓa yiwa Abba maganar cigaban karatuna ba, haba Mama ke wacce irin uwa ce?" Mama batace mata komai ba ta shige ban ɗakin dake cikin ɗakinta, Murja tabi Maman nata da kallo tanajin inama ba itace ta haigeta ba, nadama ta daɗa shigarta sosai na abinda ta aikata nasoma istigifari tana neman yafiyar ubangiji. Musty bai wani jima a waje ba yakoma gidansa yatarar Aimanah na barci ya koma falo ya zauna yana kallo duk minti goma saiya leƙa ɗakin da Aimanah ke barci yaga kota tashi, yanzuma lega wan yayi yatarar tashinta kenan tana kokarin sakkowa daga kan gadon, taimka mata yayi ta mike ya haɗata da jikinsa "Kinsha barci fatan kin tashi lafiya" batace masa komai ba tasake shigewa jikinsa sosai, kwalin waya ya ɗakko daga kan madubi ya ɗora mata kan hannunta, rufe ido tayi ta buɗe su tarwai kan kwalin wayar da murmushi saman fuskarta "Iphone wow, masha Allah ina godiya sosai Yah Musty Allah yakara arziki mai albarka" "Amin" yafaɗa yana shafa kwancancan gashin kanta daya sha gyara sai tashin kamshi yake "Muje falo kisa sim ki haɗa wayan" yana rikeda ita har suka karasa falon ya mata mazauni saman kujera shi kuma ya zauna kasan carfet yana kallonta ta buɗe wayar ta cirota daga kwali farin ciki sosai yagani shimfiɗe kan fuskarta, ya karɓa ya sama mata screen gart da wayar tazo da shi a kwalin ya mika mata ta kunna wayar "Wow Yah Musty kalli gaskiya wayar nan tayi kyau sosai" "Nifa banason Sunan nan maye wani yah Musty dan Allah" "To baby" "Yawwa na karɓi wanan nice name" rungume Musty tayi ta sumbaci laɓɓansa "Wow Reina sake sake dan Allah please" Aimanah rufe fuskarta tayi da tafukan hannunta tana dariya, ya hawo saman kujerar ya haɗeta da jikinsa yana sauke numfashi, sun jima rungume da juna, kafin aka fara looking na kofa, ta tashi zataje ta buɗe yadawo da ita ya zaunar da ita saman cinyarsa "Karki buɗe ko waye zai gaji ya koma baza'a ɓatamin wannan yanayin ba" "Musty zakuzo ku buɗemin ko saina saɓa maku" suka jiyo muryar Anty Hasana tana faɗa, da sauri Musty ya saki Aimanah ya nufi kofa yama magana a hankali "Kai Anty kin ragemin jin daɗi fa Allah yasa Dr yau ya tattaraki ku koma inda kuka fito" buɗe kofar yayi ta sakar masa rankwashi a ka tana hararar sa ta wuce sa zuwa ciki, Shaheed da Rumana suka biyo bayanta suna rikeda manyan ledoji a hannunsu [2/13, 4:44 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na Ashirin da ɗaya* Aimanah ta gyara kwanciyarta saman kujera tana kallon Anty Hasana dake mata kallon tausayi "Sannu Aimanah" kai kurum Aimanah ta ɗaga tana kokarin tashi zaune, "A'a Aimanah basai kin tashi ba yi kwanciyarki ki huta, nima ba zama nazo yi ba zuwa nai namaku sallama Dr ya takura sai mun tafi yau ga Rumana nan, na barta gidan Ana zata kara maku kwana biyu kafin agama mata shirin makaranta ta tafi" "Anty yanzu tafiya zakiyi?" "Ya zanyi Aimanah, umarni daga sama, ba yanda zanyi" "To Anty Allah ya sauke ku lafiya" musty yafaɗa yana kallon Antyn "Daman kai ai so kake na tafi na takura maka ko? toga kanan ga Aimanah nan, Allah yasa nan da wata tara mudawo suna" "Mom" Rumana tafaɗa tana kallon Anty Hasanan "To uwata hanani magana" ta tashi tana lekawa ko ina na saman tana dubawa kamar yaune zuwanta gidan na farko, ta juya zata fita bayan tabawa su Rumana umarni subar ledojin anan na Aimanah ne, Aimanah ta ruko hannun Rumana ahankali tace "Rumana inason magana dake fa" "To Anty gobe zan zo muyi magana" kai kurum Rumana ta ɗaga tabi bayan su Anty da Musty da suka sauka kasa, Akasa suka sami Sumayya ta fito daga kicin ɗinta batare da Anty Hasana ta tsaya daga tafiyar da take ba takewa Sumayya magana "Sumayya ga Amarya nan Allah yabaku zaman lafiya sai ayita hakuri mu munkoma inda muka fito" Sumayya batace komai ba tabi Antyn da kallo wacce suka fice tareda Mustapha da alama magana suke mai mihimmanci, Rayuwa sosai taima Aimanah daɗi a gidan Mustapha sosai yake bata kulawa ko wanne motsinta akan idanunsa kauna tattali da soyayya ba kalar wacce Musty bai bata ba a ƴan kwanakin da sukayi tare, ko ƙasa baya barinta ta sauka da kanta goyata yake a bayanta har kasan, sau biyu idanun Sumayya na gane mata Musty ya goyo Aimanah a bayansa zuwa kasa, takanyi takaici ta shiga damuwa hakan yasa ta nemi izininsa akan tanaso zataje katsina, ba musu ya amince mata, tafiyarta tabasa damar ɓarje amarcinsa son ransa komai tare suke cikin kwanciyar hankali da kaunar juna. Abas ya kalli hajiyarsa dake kuka sosai ganin yanda Abbas ɗinta ya rame ya yi baki sosai dama can shiba fari bane amma bayada duhu kamar yanzun ya wani tara suma kamar wani ɗan sudan, "Abas kaga yanda ka koma?" ashe baka ɗauki maganar dana gaya maka ba" "Hajiyata na ɗauka mana naji maganarki zuciyata ce ta kasa jure rashin Aimanah, Hajiya idan na mutu ki gayawa Aimanah ina mata fatan alkhairi, kice nace tabi mijinta su zauna lafiya" Hajiya tasake fashewa da kuka tana rikeda hannun Abas "Abas ka dai..."Ya isa Baba kayi shuru dan Allah, karka fama inda kemin ciwo, please Baba" Alhaji wada ya goge kwallar data zubo masa yana kallon yaron nasa cikeda nadama "A'a Abas ka barni nayi magana, kabarni na nemi yafiyarka" "Yafiyata kuma Baba, ka isa dani ne shiyasa ka yanke hukuncin da kaso, nariga da na ɗauki kaddara ko haka bata faru ba daman can Aimanah ba matata bace kamin addu'a nacika da imanai" "A'a Abas kadaina faɗar haka dan Allah, ka mutu ina zansa kaina yaya zanyi da rayuwata, bazaka mutu ba Abas kai zaka sakani a kabarina insha Allah" likitane ya shigo yana sanye da kakin sojoji ya haɗa allura yana kallon Abas ya ce "Captein zan maka allurar barci" "A'a Uwaeer karka min allurar nan ka barni na kalli fuskar Hajiyata gani nake kamar yinin yau kaɗai ya ragemin a rayuwar duniya" uweer ya ajje alluran yana kallon Abas "Captein kadaina faɗar haka cuta ba mutuwa bace anyi nasara jininka ya koma dai dai dan Allah karage damuwa ni dakai duk musulmai ne munyi imani da kaddara mai kyau ko mummuna" "Nagode Dr, ko nace Captein" dariya Uweer yayi yayiwa su Hajiya sallama ya fita, Aimanah tasawa kofar shigowa samanta key ta zare kay ɗin ta koma ta zauna kusada Rumana wacce ke kallonta da mamaki "Wai yaya Aimanah mai kikeyi haka ne kin rufe ko ina kin wani saki labulaye yanzu kuma kin sakawa kofa key Yayanmu fa yana gidan Ammi sanda na fito yana shirin tahowa nan shima fa, ki buɗe kofa karya zo yazaci ma wani abin" Aimanah tayi tagumi tana kallon Rumana hawaye suka zubo daga idanunta ahankali ta goge hawayan "Rumana inason Abas, nasihar da Daddy yayimin randa za'a kawo ni gidan nan ita tasa na kwantar da hankalina na karɓi Musty a matsayin miji na rungumi kaddarata, Rumana inason sanin halin da Abas yake ciki, ina kuma rokon wata alfarma a gareki" Aimanah ta karashe maganarta tana saka hannuwanta cikin na Rumana "Rumana ina rokonki alfarma ki auri Abas nasan bakida saurayi bakida kowa wanda ke sonki" jikin Rumana ne yahau ɓari tana kallon Aimanah ta zare hannunta daga cikin na Aimanah ta dafe bakinta🤭tareda zare idanu😳ta mike tsaye tanaja da baya baya "Ni wai haba Allah ya kiyaye na auri wanda kika so haba Yaya Aimanah" Aimanah mikewa tayi ta dawo kusa da Rumana ta tsaya tana sake haɗa hannunsu "Alfarma na nema Rumana ki taimaka kimin wannan alfarma tunda abin nan yafaru nakeji inama inada kanwa na bawa Abas na fara hasaso Surayya sai na gano suna soyayya da yaya mas'ud, tunani na karshe kwakwalwata ta tsaya a kanki, zakiyi farin ciki Rumana Abas mutum ne yayi ta ko'ina ina matukar maki sha'awar auransa, kamar yanda na gaya maki a baya har akai kwana biyar da auranmu da Mustapha banji a raina zanyi rayuwa da shiba, na kudurce a raina saina kashe auran nan na auri Abas amma girma da kimar Daddy tasa na manta da komai na jure zan zauna da Musty da ayanzu nakejin sa a zuciyata fiyeda Abas kawai dai ina tausayin Abas daga sanda kika amsamin kin amince da auran Abas zuciyata zata nutsu nasami nutsuwa da kwanciyar hankalin da zan bawa Mijina kulawa" "Yaya indai har inna auri Abas zakiyi farin ciki a gidan Mustapha na yarda zan aure sa amma inyace baya sona fa?" "Bakida damuwa da wannan bani wayarki" Aimanah taja hannun Rumana suka zauna saman kujera tana gayawa Rumana lambar Abas tana sakawa a wayarta tai call saida ta kusa katsewa sannan yai picking call ɗin Rumana ahankali ta ce "Hello" da sauri Abas dake kwance saman gadon asibiti ya mike zaune ya ce "Haya"..dafe kansa yayi kana yace "Aimanah" yafaɗa da raunanniyar murya "Ba ita bace Rumana ce" wani bakon yanayi yaji na daban a zuciyarsa daya kasa banbance na mene "Ga Yaya Aimanan zakuyi magana" "Abas" Aimanah tafaɗa muryarta na rawa kamar zata fashe da kuka "Aimanah ya kike ya mi..." sai kawai yayi shuru yakasa karasawa "Abas ya kake fatan kana cikin aminci" mikewa tayi ta shige bedroom ɗinta ta zauna "Ina lafiya Aimana ina mijinki kika kirani a waya?" "Baya nan" "Mai yasa zakiyi haka ki fara neman izininsa sai muyi magana" "Ka bari muyi magana Abas tanada mahimmanci, nasan matsayina a zuciyarka hakan yasa zan roki wata karamar alfarma a wajanka" "Wacce alfarma faɗi Aimanah ko wacce iri ce zan maki insha Allah" "So nake ka auri Rumana" "Rumana" ya maimaita da sauri "E! Ita" "A'a Aimanah dan Allah karki ce haka" "Idan kamin haka raina zaiyi daɗi zata kula da kai nasan Rumana batada wata matsala zakaji daɗin zama da ita" hmmm Abas ya sauke numfashi "Idan ni na amince ita fa" "Nagama magana da ita" "Shikenan na amince Aimanah, Allah yasa tanada halaye irin naki" "Tanada fiye da nawa ma" "Ki kasance cikin Aminci Aimanah ki zauna da mijinki lafiya ina maku fatan alkhairi" "Nagode, wannan lambar Rumana ce dan Allah naji labari mai daɗi da zai sani kwanciyar hankali" "Kamar ma kin samu ne Aimanah ki saka mana ranar bikinmu" "Ku fara dai daitawa tukunna san samu karya wuce nan da wata guda" "Da wuri haka" "E!" "Yaya Aimanah kizo ki buɗe yayanmu na buga kofa," tajiyo muryar Rumana tana faɗa daga inda take, saurin sallama tayiwa Abas ta fita, taje ta buɗe kofar, yana shigowa ya eungumeta a jikinsa "Maye na rufe kofa" yafaɗa yana kallon cikin idanunta kamar mai son gano wani abu "Kuka! kukan me kikayi?" kokarin kwace kanta take amma ta kasa duk kunya ta kamata ganin Rumana na cikin falon, "Bazaki ce komai ba Aimah" ta buɗe baki zatayi magana ya haɗe bakinsa da nata da sauri Rumana ta salallaɓa tabar falon kar taga abinda yafi karfin idanunta, Musty zama yayi kan kujera ya ɗorata saman cinyarasa yana cigaba da abinda yake, "Baby Rumana na nan fa" "Na ganta na guma ga sanda ta fita" wai gawa Aimanah tayi tana kallon kujerar data bar Rumana a zaune taga wayam ba kowa😂 "Kinsa ta gudu kin bata kunya" "Kabata dai ta faɗa tana lakace masa kumatu" "reina na gaji zumu shiga daga ciki mu raba gajiyar nan" "Gobe sunday fa nasan zakace zaka tafi ga Sumayya bata dawo ba" "Munyi waya ɗazu sai friday zata dawo, goben ai jirgin dare zanbi ko zakizo mu tafi tare?" "A'a bazani ba nima monday hutuna zai kare" "shikenan" musty yafaɗa sanda suka ahiga ɗakin, hannu yasa ya ɗau wayar Rumana daya gani ajje saman gado, ya juya wayar yana kallon Aimanah datayi kasa da kanta "Wayar wace?" "Ta Rumana ce" "Rumana nan kika kawo ɗakin kwanan mu?" "A'a nina yi waya da ita" "Ina taki wayar?"dawa kuma kikai waya" "Yah Mus'af" tafaɗa muryarta na rawa, "A'a reina nasanki gaba da baya zan iya rantse maki baki faɗa dai dai ba, ba da Mua'ab kikai waya ba, bana son karya akomai ki rinka gayamin gaskiyya komai ɗacinta" "Da Abas nayi waya" Aimanah ta faɗa kanta a kasa muryarta na rawa, Musty ya mike tsaye ya kama kugu yana kallon Aimanah, jikinsa a sanyaye ya koma ya zauna "Aimaahh maina maki nai haka kin kasa mantawa da A" "Ba wani abu nace masa ba nagaya masa ne ya nemi Rumana da aure" "Bana so karki sake magana da shi" "Insha Allah, bazan sake ba," "And karki sake ɓoyemin komai, mu rinka tattauna damuwarmu mu samu mafita tare" "Insha Allah baby" tafaɗa tana sake kwanciya ajikinsa. Abas da aka sallama suka koma gidansa tareda su hajiya komai yagaya mata yanda sukayi da Aimanah "Kai ya kake gani?" "Na yaba da hankalin yarinyar, na kuma karɓi rokon Aimanah amma ki gayawa Baba yaje yafara magana da iyayanta, karki gaya masa Aimanah ce tamin tayinta ki faɗa masa ni na ganta nace inasonta zan gayawa Rumanan da Aimanar subar maganar nan a tsakaninmu" "Shikenan Abas nayi farin ciki da hakan Allah ya zaɓa abinda yafi alkhairi" "Amin" yace bayan ya kwantar da kansa saman kujera, Aimanah tunda yamma tayi tafara kukan shagwaɓa musamman sanda taga yana haɗa kayansa cikin trolly, kwanciya tayi saman bed tana fashewa da kuka ganin Musty ya ɗauki jakarsa zai tafi, cikeda damuwa yadawo ya zauna kusa da ita yadafe kansa, can kuma ya mike ya buɗe wardrove yafara zuba kayanta a trolly "Nifa bazani ba," tafaɗa cikin kuka "Toya kike so nayi kin tisa ni a gaba kinamin kuka ku tashi kawai mu wuce legos ɗin tare" "Bazan bika ba hakan ai saiya zama rashin adalci ga Sumayya anan ni nabika can ai bamu kyauta mata ba koni akayiwa haka bazanji daɗi ba....✍🏻 [2/13, 4:45 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na Ashirin da biyu* Jiyo sallamar Ahmad a falo yasa Musty ya fito yana rikeda Aimanah a jikinsa, "Yadai malam dogo ina ɓata lokaci ko?" Ahmad ya taɓe baki yana nuna masa agogo tareda yamutsa fuska "Saura yan mintuna fa jirgi yatashi" bai tsaya jin mai Musty zai faɗa ba yaja trolly ɗin Mustyn yafita, Musty ya koma ɗaki ya ɗakkowa Aimanah hijab yasa mata "Reina kimin rakiya zuwa airport" "Baby, bazani ba kuka zanyi kabarni kawai anan" zare jikinta tayi daga nasa tayi baya tana ɗaga masa hannu alamar bye, tashige ɗakinta ta rufe da makulli ta sulale a kasa tana fashewa da kuka, yana jiyo kukan nata hakan yasa ya juyo zuwa kofar "reina please ki buɗe mu tafi tare kin sani bana son kukan nan naki" tana jinsa yakaraci bugunsa ta kyalesa, fita yayi inda Ahmad da shaheed ke jiransa "Yayanmu ka ɓata lokaci da yawa fa, Allah yasa ma ba go slow a hanya karya rike mu" "Ahmad kabi ta gadon kaya ina jin nan ba goslow sosai" Ahmad baice komai ba aikinsa kawai yake na tuki, Ammi jin ana kiran sallar insha yasa ta kalli Surayya da Rumana "kuyi salla kuje ku taya Aimaah kwana" da sauri Rumana ta kalli Ammi "Ammi mu tayata kwana kuma?" "E! haka nace Mustapha ya koma legos yau" "Ammi ai na zaci tare zasu tafi" Surayya ta faɗa tana danna wayarta da murmushi a fuskarta da alama chat take da Mas'ud "Nima haka naso amma Aimanah ta kawo dalilin dana aminta data zauna anan ɗin" ba wanda yasake cewa komai sai salla da suka muke sukayi abincin dare suka ci sun gama ci kenan wayar Rumana tayi kara, gabanta ne yai wata irin bugawa ganin lambar Abbas na yawo a fuskar wayar, "Abbas" tafaɗa a hankali, mikewa tayi tana satar kallon Ammi ta wuce bedroom ɗin Ammin "Hello Hayatie" Abbas yafaɗa yana lumshe idanu daga inda yake kwance saman bed dake cikin gidansa "Uhmm umhnm Rumana ce" Rumana tafaɗa muryarta na rawa "Na sani ai Hayatie ya kike" "Anya na can canci wannan sunan kuwa da dai ka daina faɗa" "Kin wuce haka ma a zuciyata ina kau..." shiru yayi yai saurin saka hannu ya danne kirjinsa dayaji lokaci ɗaya numfashinsa na shirin ɗaukewa "Na riga na sani daman" Rumana ta faɗa tana dariya "Kika san me? kisa a ranki Rumy kece madadin Aimanah a zuciyata" "Anya kuwa zan iya zama madadin nan" "Zaki wuceta ma insha Allah, karki faɗawa kowa cewar Aimanah ce ta haɗamu ki barshi a nina kawo kaina gareki kema kuma kisa haka a ranki" "Nasa" "Kin tabbata" "Gaske" "Bani labari" "Yana wajanku, bari zamuyi waya anjima naji Ammi tana kirana" sallama sukayi da Abbas ta sa wayar a kirjinta kana ta sumbaci wayar ta buɗe idanunta karaf idanunta cikin na Ammi da batasan ta shigo ɗakin ba, murmushi Ammi tayi tana kallon Rumana "Dawa kike waya? koma dai nasani nayi suruki Allah yasa alkhairi" Rumana da gudu ta fita daga ɗakin tana dariya, tare suka jera da Surayya zuwa gidan Aimanah suna tafe a hanya Rumana taruko hannun Surayya suka tsaya "Sury mai zakice min idan nace maki Abas ɗin Aimanah ɗazu munyi waya dashi wai! wai!! wai yana sona" Surayya ta dafa kirji "Kai nayi farin ciki matuka ke kuma mai kika ce masa" "Bance komai ba kina ganin hakan bazaija cece kuce ba a family" "Banajin hakan zata faru akwai fahimtar juna a tsakanin iyayanmu maza da mata banaji akwai wata matsala, ina maki fatan alkhairi" "Nagode matar Yah Mas'uf" dafe kirji Surayya tayi tana dariya "Ya'akayi kika sani duk ɓoyewar da muke" "To garama ku fito fili kuyi soyayyarku sabida kowa ya san inda kuka dosa" dariya sukayi gaba ɗaya kana suka cigaba da tafiya, falon a rufe da alama a rufe yake sunyi looking amma ba'a buɗe ba hakan yasa suka kira Ammi wayar Aimanah taki shiga, Saheed ne yakawo masu kay suka buɗe suka shiga. Amarya na tsaye gaban madubi sai shafa wannan goga wancan take, ta kashe ɗauri ta kalli Murjana batace komaiba ta yafa mayafi tana kallon Murja dake kwance saman gado lamo kamar mara lafiya "Dan Allah Murja kekam wai mai kike son zama ne kinbi duk kin addabi rayuwarki da tunani" Murjana bata ce komai ba saima gyara kwanciyyarta da tayi ta juyawa Amarya baya tana jinta harta fice daga ɗakin, wata haɗaɗɗiyar mota ce a fake a waje take jiran Amarya cikeda gadara ta buɗe bayan motar ta shiga tana hura baki da hanci, direban motar yaja suka bat layin batare dayace mata kala ba, kofar wani haɗaɗɗan gida motar ta faka Amarya ta fito tana karewa gidan kallo, direban motar ya fito "Hajiya ki shiga daga ciki, mai gadi zai maki jagora har zuwa cikin gidan" batace masa komai ba ta tura haɗaɗɗan gate ɗin ta shiga bako sallama, getman yataso da sauri yana tambayarta ina zataje, card ɗin hannunta ta nuna masa yace ta biyo bayansa yana gaba tana binsa a baya idanunta na kallon ko'ina na gidan, gida ne haɗaɗɗe daya sha fulawoyi ta ko'ina, kanta bai gama kuncewa ba saida ta gansu tsaye gaban kofar glass ya danna wani madanni kofar ta buɗe suka bayyana a wani kawataccan falo daya gaji da haɗuwa, sakato tayi da baki tana kallon falon da iya tsawon rayuwarta bata taɓa ganin haɗaɗɗan falo irin wannan ba, tayi hulda da manyan mata masu kuɗi na garin nan amma kam bata taɓa ganin gidan daya kai wannan haduwa ba, matar da suka haɗu a wajan boka mai suna Hanne ita ce ke sakkowa daga saman bene tana sanye da riga da wando jajaye kanta bako hula saima uban gashin doki data cika kanta, kai tsaye tana zuwa kusada Amarya hannu tasa a jikinta tana shafata tana wani lumshe idanu, getman juyawa yayi ya fita yana girgiza kai "Sannu da zuwa tun ɗazu nake jiranki ashe da gasken zaki zo" "Zanzo mana ai na gaya maki indai zan sami kuɗi zan iya aikata komai" kai Hanne ta jinjina tareda zaunar da Amarya kan kujera ta miko mata lemu a cup tace "Yawwa sha wannan bari na shiga daga ciki ga kayan abinci nan kici duk abinda kike so zan komasama inada baki ne yanzu zan sakko inna sallamesu" Amarya kai kurum ta ɗaga ta kai cup bakinta bako bisimillah ta kwankwaɗe lemun daya sha magunguna tas a bakinta, mintina kaɗan da shanye lumun nata tafara jin wani yanayi a jikinta na daban, tun tana jure yanayin har ta mike ta hau saman tasoma laluban inda zataga Hanne, Hanne dariya tayi sosai ganin Amarya na laluban inda zata ganta kenan maganin ta yayi aiki dariya tayi sosai , fitowa tayi daga ɗakin ta ja hannun Amarya suka faɗa ɗakin, Amarya ba tinanin komai ko abinda zaije yadawo ta biyewa Hanne suka aikata ma sha'a son ransu😰 Al'Mustapha takwas saura minti biyar ya isa gidansa, wanka yayi yasha tea yai shirin kwanciya gobe fitar safiya zaiyi so yake bakwai tamasa a office yasan kwanakin nan daya shafe baya nan ayyuka zai tarar jibge a office ɗinsa, yana kwanciya kewar Aimanah ta lulluɓesa wayarsa ya jawo ya danna call wa Aimanah sai dai wayar bata shiga ya kira yafi a kirga bata shiga ba hakan yasa ya kira Ammi saida suka gaisa kana ya ce "Ammi waye yaje wajan reina na kira wayanta bata shiga kodai har yanzu kukan take?" "To yanzu wacce amsa zan baka" dafe baki yayi kana yana yar dariya ya ce "Allah yakara lafiya Ammi wacce duk kika bani zan amsa" itama dariyan tayi kana ta ce "Muhammad Mustapha anya kuwa kana kamanta adalci a tsakanin Aimanah da Sumayya" Musty shafa kansa yayi yana murmushi ya ce "Ammi zan kamanta insha Allah, nabaro Aimah tana kuka ne shiyasa gaba ɗaya na damu na kira wayarta kuma a kashe" "Tana lafiya kila ko ta kwanta barci ne ta kashe wayar, ɗazu bayan sallar insha na tura mata Surayya da Rumana su kwana tare" sallama ya mata da sauri ya katse kiran, Ammi tabi wayar da kallo tayi murmushi tareda girgiza kai ta ce "Hmmm Musty kenan, Allah yabaku zaman lafiya da zuriya ɗayyiba" Musty gaba ɗaya damuwa ta mamaye sa musamman daya kira wayar Rumana yaji a kashe wayar Surayya kuma duk sanda zai kira number basy "Mas'ud" Mustapha yafaɗa yana murmushi, layin Mas'ud ɗin ya kira shima dai Number basy, dafe kansa yayi ya mike yana rike da waya a hannu yana zagaye a ɗakin, minti biyar tsakani kana ya sake kiran wayar Surayya wannan karan ta shiga, lokacin da kiran ya shiga Surayya tana kusada frige tana shan ruwa wayar na kusa da Rumana, Rumana dake dariya ta ɗauki wayar tana kallon fuskar wayar "Surry yayanmu ne" kwarewa Surayya tayi da ruwan datake sha ta fito da idanu haɗe da dafe kirji "Na shiga uku ni Surayya mai nayi kuma da daran nan?" Aimanah na dariya tamike ta shige bathroom na cikin falon, Surry na ɗaga wayar bai tsaya amsa sallamar datake masa ba ya ce "Ina reina bata wayan" "Ta shiga bathroom" "Kice ta kunna wayarta" katse kiran yayi yana kallon wayar tasa ransa ɓace, tsawon mintuna yana jera kiran wayar Aimanah amma bata shiga ransa ya kara ɓaci yasake kiran wayar Surayya lokacin suna dayan ɗakin sunyi shirin kwanciya barci, "Kai dan Allah yayarmu ki kunna wayarki nifa harga Allah innaga kiran Yayanmu gabana har faɗuwa yake saboda nasan hakanan bai kiran wayata" Surayya ta faɗi haka tana kallon Aimanah, Aimanah gyara kwanciyarta tayi ta juyawa masu baya tana murmushi, Surayya ɗaga kiran tayi "Yayanmu wallahi taki kunna wayarta fa nama rasa inda tasa wayar tata" "Sa wayar a hansfree" tayi abinda yace ɗin da sauri Aimanah tasa hannu ta toshe kunnuwanta, Rumana ta fisgo wayar daga hannun Surayya ta ɗorawa Aimanah a kunnanta suka ruke hannuwanta "Aimanaaa" yanda yaja sunan yasa taji wani yanayi na daban a jikinta, gaba ɗaya jikinta yayi wani irin sanyi "Aimanaaah" "Uhmmm" tafaɗa a kasalance "kinaso na biyo mota a daran nan na dawo kano ko? kinsan yanda nakeji kuwa Aimana kinsan yanda sonki yake azabtar da ruhi da gangar jikina, kinsan yanda kewarki ta addabi zuciyata kuwa Aimaaah, na rokeki duk laifin da zanyi kar a hukunta ni da rashin jin sassanyar muryar nan taki please Aimahh, gobe ki biyo jirgi kizo kona samu nutsuwar yin aiki" "To kadawo kano da aikin mana" Aimanah tafaɗi haka tana turo baki gaba "Zanso hakan ta kasance zan kuma gwada Allah yasa su min transfer" "Nifa barci nakeji" "Haka zamuyi dake bama ko tambayya ya hanya ya nake" katse kiran tayi tareda kashe wayar Suraiyan tasa ta kasan filo "Yaya Aimana nayi magana" "Kice me?" "Ni sai nake gani kamar baki kyauta ba, bafa ke kaɗai bace a wajan mijin nan naki yana bin kanki kinata masa yawo da hankali karfa ya karkata ga Anty Sumayya kizo kuma kina mana koke koke" dariya Aimanah tayi tana sake gyara kwanciyya ta ce "Surayya kenan nasan abinda nake ko zuba idanu kawai" "Yaya maganar Surayya fa abar dunawa ce" "Abbas ya kiraki?" tafaɗi haka tana kallon Rumana, "Ba wannan maganar muke ba," Rumana tafaɗa itama tana gyara kwanciyarta, Surayya ma filo taja ta kwanta tana binsu da kallo. [2/13, 4:45 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na Ashirin da uku* Alhaji farouk ya kalli Alhaji Abubakar idris wada dayake ta faman basa hakuri, murmushi Alhaji farouk yayi kana ya ce "Alhaji ni daman ban rike ka ba kaine ka ɗauka da zafi ko lokacin ɗaurin auran Aimanah ma sai da nace mu tsaya mu fuskanci juna amma kaki yadda, yanzu dai kaga yanda abubuwa suka kasance Allah yasa haka shiyafi alkhairi garemu gaba ɗaya, yaya Abbas yake" "Yana lafiya yanzuma shiya taso ni daman kuma ina son zanzo nabaka hakuri" "To Allah dai yasa lafiya" Alhaji farouk yafaɗa yana gyara zamansa saman kujera "Lafiya kalau ya tasoni ne kan maganar dai auransa yacemin akwai yarinya kanwar Aimanah Rumana in wani bai rigasa ba amasa izini" Prop yafaɗaɗa murmushinsa yana faɗin "Alhamdulillah masha Allah nayi matukar farin ciki da haka sai dai ban sani ba ko akwai maganar wani akanta, amma bari na kira mahaifinta muji" Alhaji ya ɗanna wayarsa ya lalubo lambar Dr Makthar mahaifin Rumana kiran farko Dr dake zaune cikin ɗakin sa shida Anty Hasana ya nunawa Anty Hasana fuskar wayar "Abin mamaki kinga kira daga prop da yammacin nan" ɗaga kiran yayi tareda ruko hannun Anty Hasana ya jawota jikinsa "Barka da yamma prop" "Yawwa barka dai Dr ya gida ya Qatar?" "Alhamdulillah sai godiya" "Masha Allah, daman kan maganar Rumana ne...gaba ɗaya yanda sukayi da Alhaji wada idris yafaɗa masa jimm yayi kafin can kuma ya ce "Prop banida abin cewa kan maganar nan indai har Abas yayiwa Rumana to nabasa ita Allah ya basu zaman lafiya, nabar ragamar komai a hannunka har ɗaurin aure ka ɗaurawa Ruma aure Allah yasa albarka" Anty hasana mikewa tayi daga jikinsa ta zauna tana lega fuskar mijin nata dan sarai taji yanda sukayi "Dr da wirwuri haka Ruma fa karamar yarinya ce duka duka yaushe na haifeta ko Mujahid fa shekarunsa ashirin fa yanzu" dariya Dr yayi "Rigima dai rigima ke ko yaushe zaki girma sanda na aure ki shekarunki nawa?" dariya tayi ta ɓoye kanta a kirjinsa tana dariya sosai, shigowar babban yaronta Mujahid yasa ta cire kanta daga kirjin Dr "Alhaji kaji yanda mukayi da mahaifin Rumana na yarda da tarbiyar Abbas tun a farko na basa ƴata Aimanah a yau na sake basa Ƴata Rumana na tsaida biki nan da makonni biyu masu zuwa lefanku daman yana nan, yanzu sun zama na Rumana sadaki kawai muke bukata daga gareku" "Prop nagode sosai da wannan karamci dakayi min nagode Allah yasaka da alkhairi" "Amin" prop yafaɗa sukayi sallama, kafin wani lokaci labarin tsaida ranar bikin Rumana ya karaɗe dangi gaba ɗaya kowa murna yake sosai musamman Aimanah, Abbas ne kawai gashi nan gashi nan shi bazaice yana farin ciki ba haka bazaice yana murna ba. Mustapha gaba ɗaya yakasa gane kansa baijin nutsuwa sam atare dashi ko yaushe Aimanah aimana burinsa kawai ya gansa gashi ga ita, ita kuma taki basa haɗin kai gaba ɗaya ko kiransa bata ɗagawa hakan yasa yau laraba yabi jirgin yamma zuwa kano, Aimana tagama gyara ko ina na gidanta sai tashin kamshi yake, wanka tayi ta shirya cikin doguwar rigar yar maroco ta yane kanta da mayafi ta feshe jikinta da kalolin turaruka masu saukin kamshi falo ta dawo ta zauna tana danna wayarta, haka kawai yau takeji kewa dason jin muryar Musty ko ganinsa, tunda ta zauna a wajan kiran layinsa take amma bata shiga, karar buɗe kofa alamun mutum ya shigo baisa ta ɗago ba bare taga wace tasa a ranta ma Rumana ce dan bata daɗe da fita ba, Surayya bata nan tana makaranta, "Amaryar Abbas bani wayarki na kwada kiran Baby gaba ɗaya wayarsa bata shiga kuma Allah so nake naji miryarsa ke ni ganinsa ma nake son yi" ɗagowar dazatayi sukai ido huɗu da Mustapha, zaro idanuwa tayi tareda buɗe baki zatai ihu yai saurin saka hannunsa saman bakinta alamar tayi shuru, idamunsa cikin nata harya zauna saman kujera "Kin wahalar dani reina kin kin azabtar da zuciyata Alhamdulillah nagodewa Allah kema yanzu kinji yanda naji" "Yi hakuri to" hannu yasa ya lakace mata kumatu yana harararta "Bakiji kewata ba" "Naji sosai ma" "Ban yarda ba" yafaɗa yareda ɗaukarta gaba ɗaya suka shiga ɗaki. Sumayya tunda taje Katsina tana gidan babanta wanda tun tuni yasake aure ya auri matarsa Ramatu mace mai kirki da son mutane, kusan ko yaushe tana ɗaki a kwance cin abinci ke fitowa da ita daga ɗakin, yau tun safe take shirin tahowa kano ta haɗa komai nata jira take ayi a azahar taje tasha ta hau mota, gaba ɗaya batada kuɗi tana son tambayar Mustapha kuɗi tana tsoro batason ya zargi wani abu daban daga danginta, App ɗinta na opay ta shiga ta duba taga sauran nawa take da shi in bazasu isheta zuwa gida ba ta kira Murja ta roketa ta tura mata kuɗin mota, murza idanunta tayi ta rufe su ta buɗe tasake rufewa ta buɗe kuɗindai suna nan kamar yanda ta gani kasa ta duba taga waya mata transfer mai kauri irin haka, "Mustapha Kamal Sarina" tafaɗa a fili, rungume wayar tayi hawaye na zubowa daga idanunta, tarufe idanun tana cigaba da kuka kasa kasa, kiran daya shigo wayarta yasa ta goge hawayen fuskarta tai picking call ɗin "Ina kwana" "Lafiya kalau Sumy ya kike ya katsinan, ga kuɗi nan na turo maki ki dawo gida da wuri yau zan dawo kinsan wajanki zan sauka bana son na rigaki shiga gida" "Insha Allah" tafaɗa murya a raunane, bai jira abinda zatace ba ya katse kiran, ɗakin babanta taje ta masa sallama yabata dubu goma aciki tayi kuɗin mota zuwa gida, falonta ba wani kura sosai ba kamar ɗakunan ta ba da sukai kura da alama Aimanah na kula da falon, jakarta kawai ta ajje ko wanka batayi ba ta shiga kicin, komai akwai a kicin ɗin sosai, turus tayi taja ta tsaya bayan ta gama duba komai, hawaye suka zubo mata na takaicin duk waɗan nan abubuwan bata iya komai ba banda dahuwar farar shinkafa da mai da yaji bata iya komai ba, batajin ma ita nan rayuwarta ta taɓa haɗa miya da kanta, komawa tayi ɗakinta ta kira wayar Murjana, Murja dake tsaye a ɗaki tana kallon Amarya dake waya tana kashe murya taga kiran yayarta ta ɗaga da murmishi "Anty kin dawo?" "Nadawo ƴar uwa zo dan Allah" "Ok gani nan shigowa" Sumayya ta koma ta zauna saman kujera tana jin kamar ta haura saman Aimanah su gaisa kamar kuma kartaje, haka ta zauna har sanda Murja tazo, Sumayya hannunta taja zuwa kichin suka tsaya Murja na karewa kicin ɗin kallo, "Sumayya kalli kicin ɗin nan dan Allah gaba ɗaya a hargitse kamar ba mace ke amfani da shi ba, ke komai naki ba tsabta shiyasa kuke faɗa da Mama" "Murja ba wannan bama yau Musty zai dawo so nake na masa girki na rasa maizan dafa nifa inba shinkafa fara ba sai indomie su kawai na iya dafawa" dariya Murja tayi kana ta ce "Cab ina zan tsaya ban iya girki ba, kema Allah Sumayya sake kikayi kika biyewa son jiki irin naki bakya komai, dai dai da sharan ɗaki sai mama tayita fama dake kana zakiyi" "Duk zan daina son jikin nan yanzu dai kwadamin yanda zan yi jar miya saina dafa faran shinkafa" "Shinkafa kuma mijin naki zai dawo zaki masa wani shinkafa kamar a kauye" "To Murja mai zanyi ni ban iya komai ba" Sumayya tafaɗi haka tana ɗora tukunya saman gas, Murja ta buɗe firij ta ɗakko naman sa ta wanke kana ta soma yankawa, Sumayya na kallonta harta gama yankawa ta sake wankewa ta ɗora a tukunya ta zuba albasa da kayan kamshi komawa tayi ta sake ɗebo kayan miya a frezar ta wanke su ta markaɗa a blanda, ita ta haɗa miyan, lasar miyan tayi a bakinta da sauri ra fito daga kicin ɗin ta faɗa toilet ɗin dake falon tafara kwarara amai, gaba ɗaya hankalin Sumayya yatashi ganin yanda Murja ke amai tana kallo ta gama ta wanke fuskarta suka fito "Sumayya jiya da yau olsa ke wahalar dani wallahi da zaran naci wani abu mai maiko sai amai" Sumayya ta zubawa Murja idanu can kuma ta ɗauke ganinta daga kanta ta mata sannu suka koma kicin ɗin, kayan da suka ɓata Murja ta tattara zata wanke Sumayya ta ɓata rai "Da kinbarsu sai anjima mu huta" "Zaki gayyato kudaje kenan kicin ɗinki, ai da zaran kin gama aiki yi wanke wanke ki gyara ko ina shine dai dai" Murja ta kalli agogo taga bakwai saura na yamma maza Sumayya jekiyi wanka ki gyara jikinki Yayanmu jirgin shida na yamma yake biyowa kar yazo ya ganki haka ba wanka" "Kai Murja kefa daɗina dake kamar wata kwaɗuwa haka kike da wanka ɗazu fa na yi wankan da zan tawo kano" Murja rike baki tayi "Cab zauna nan to kar kiyi wankan ki fesa turare kyaji wasu sunayi ai" "Zan canza kaya fa innayi alwala" Murja barin wanke wanken da take tayi taja hannun Sumayya zuwa ɗakinta ta turata bathroom "Kinsan Allah Sumayya sai kinyi wankan nan" "To sani nayi dole uwata" Murja bata kulata ba ta fice daga ɗakin. Aimanah tun safiyar juma'a data tashi tayi sallar asuba bata koma barci ba, aiki tayi sosai a gidan itada Rumana zaman kujerun falon ma saida suka gyara haka labulaye suka saka wasu kana suka shiga kicin samosa sukayi da metpie da lemun abarba suka saka a firij wanka sukayi da la'asar suka fita, karan farko kenan da Aimanah ta fito daga gidan tun randa aka kaita, wajan saloon sukaje aka gyarawa Aimana gashinta aka mata jan lalle tayi kyau sosai sai gafda mangariba suka koma gida Aimanah wanka ta sake ta shiga kicin tana kokarin ɗora tukuya Rumana ta katseta da "Yaya naga kamar fa Sumy tadawo" "Data dawo sai akayi yaya sai akace karna farantawa mijina" "Ni bance ba amma nayi tunanin wajanta zai sauka" "Koya sauka wajanta koya sauka nan banda damuw akai abinda kawai na sani shine sai yaci abinci anan wallahi" tafaɗa tana haci "Lafafa min yayarmu" "Kece da abin haushi Rumana har kinsamin damuwa ma, nama fasa yin fride rice ɗin" ta kashe gas ɗin ta dawo falo ta zauna, wayar Shaheed ta kira yana ɗagawa ta ce "Shaheed zo" bata jira amsar saba ta katse kiran, mintina kaɗan ya shiga gaba ɗaya abinda suka soya ta ɗakko ta mike masa "Shaheed ungo rabawa almajirai" ya kalleta ya kalli abinda take mika masa ya ce "Na rabawa almajirai kuma" "E! haka nace ko bazakayi ba" tafaɗa a tsawace Shaheed ya mike zai fita Rumana dake kallonsu ta ce "Yah Shaheed na Yayanmu ne fa kawai daga nace mata yaya wajan Anty Sumy zai sauka shikenan tahau masifa da fushi" zama ya koma yayi yana kallon Aimanah sai kuma ya ɗauki babban flask ɗin ya koma da shi kicin harya juya zai fito sai kuma ya ɗauki meatpie ɗaya yafito yana ci Aimana hararansa tayi "Wayace kaci abin mijina" dariya Rumana da Shaheed sukayi a lokaci ɗaya "Kefa Yaya Aimana rigima ce dake sai kace karamar yarinya kodan gado ba karambani ba na tini ke ɗin ƴar Anty Hasana ce" dariya sukayi gaba ɗaya sai kuma aka ware aka fara hira har zuwa sanda aka fara kiraye kirayan sallar insha Shaheed da Rumana tare suka fita zuwa gidan Ammi ita kuma Aimanah ta shiga ɗaki zatayi sallah, Shaheed da Rumana na tafe a hanya Shaheed yace "Gaskiyya meatpie ɗin nan yayi daɗi waima maiyasa na ɗauki daya kawai" "Yai daɗi sosai danma bakaci samosa ba" Shaheed tsayawa yayi "Rumana kodai mu koma to" dariya Rumana tayi harda sunkuyawa "Kaje man ka haɗu da Yaya ai yau kam zanso ace ina gidan nan Yayanmu zai dawo nasan akwai dirama" "Yaya Aimana da yayanmu na matukar burgeni har jinake inama akwai sauran wata macan kara dana kama" "Kajira na haifa maka" "Cab Allah ya kyauta badani za'ayi wannan abin kunyar ba tayita tacemin uncle kamar a school" dariya sosai Rumana tayi, suna gafda shiga cikin gida ta kofar baya suka hangi shugowar motar yaya Ahmad ta get na gidan Musty "Boss yadawo" Shaheed yafaɗa yana dariya ko mu juya ne, juyawan kuwa sukayi wajan motar Shaheed ya buɗewa Musty murfin motar yafito, ɗan risinawa Shaheed yayi alamar girmamawa ya ce "Barka da zuwa yayanmu" "Autan Ammi barka dai" Musty ya faɗa yana sha kan Shaheed "Yayanmu barka da hanya" "Yawwa barka dai Amaryar Abbas" rufe fuska Rumana tayi tareda kwasa da gudu tabar wajan, Shaheed ne ya ɗebi ledojin dake zube a bayan motan mai ɗauke da tambarin wani babban kanti dake nan kano ya shiga da su cikin falon Sumayya, yana fitowa shi kuma Musty zai shiga "Sannu dawo ka shigawar dasu Ammi tsaraban su" Shaheed komawa ciki yayi yana kallon Musty ya ajje ɗaya ledan saman kujera yana murmushi a hankali yace "reina" ya ɗakko babba daga cikin ledojin yace "Ka kaiwa Momy kace ga tsarabansu" karɓa Shaheed yayi yana leka ledan dake ajje samab kujera yace "Yayanmu wannan inta yaya Aimah ce bani na mika mata sama" "Kai zaka kai min?" shaheed sosai kansa yayi kana ya ce "Daman yayanmu wani meatpie naci mai daɗi nakeso na koma nasake ci" "Kai akayiwa kenan?" "Ina ni wane mutum" "To wuce ka tafi" Musty yafaɗa haleda talle masa keya "Yayanmu da zafi fa, ka ajjemin samosa biyu ko kuma na gayawa Ammi ka zane ni" dariya Musty yayi tareda shiga ɗakin Sumayya yana rikeda leda ɗaya a hannun sa, Sumayya rungumesa tayi tana faɗin "Sannu da dawowa dear" "Yawwa sannu ya kike ya hanya fatan kin baro kowa lafiya" "Lafiya kalau" ta jima a jikinsa kana ya janyeta yana faɗin "Muje ɗakina ki haɗamin ruwa wanka nakeso nayi nai sallah saina ci abinci" "Kafara cin abincin to" "Inna dawo daga tafiya bana iya cin komai sai nayi wanka kaimin ruwan wankan dai" futa sukayi tare zuwa ɗakinsa idanunsa na kallon kofar hawa sama, ajjiyar zuciya ya sauke yana danne zuciyarsa kan abinda yakeji a zuciyar, bayan yayi wanka sallah yafita masallaci yayi ya biyo ta gidab Ammi suka gaisa da su momy da Ammi ya leka ɗakin Amarya zai gaidata Murjana ke sanar masa bata nan ta fita, sanda ya koma Sumayya na tsaye gaban teble tana jiran shigowarsa, loma ɗaya yakai a bakinsa yayi murmushi yana kallon Sumy "Abinci tayi daɗi sosai daman har haka kika iya girki" Sumayya ta rufe idanunta da hannunta tana dariya, bayan cin abincin nasa sun jima suna yar hira a zaune a wajan, gaba ɗaya zuciya fa ruhinsa suna ga Aimanah so yake yahau saman amma yakasa bayaso Sumayya taga kamar bai kyauta mata ba, tare suka shiga ɗakinsa ya ɗauki wayarsa missed huɗu yagani na Aimanah gaba ɗaya sai yaji damuwar tasa ta ninku mikewa yayi "Bari naga kanwarki banji motsinta ba" batace masa komai ba tabisa da idanu har ya fita, Aimanah ta gama cika da batsewa na rashin ɗaga kiranta da baiyi ba, bata sanma yadawo ba hakan yasa ta rinka kiran layinsa a tunaninta bazai dawo ranar ba hakan yasa ta kwanta a ɗakin da suke kwana tareda su Surayya tana jiran zuwansu, Falon shuru ba motsin komai sanda ya hauro saman kai tsaye bedroom ɗinsa na saman ya wuce inda yake zaton tana can sai dai bata nan ya fito ya shiga ɗayan ɗakin tana kwance saman bed tana danna wayarta ɗagowa tayi taga waye ya shigo ta gansa tsaye bakin kofa ya buɗe mata hannayansa, ajje wayarta tayi ta je ta shige jikinsa, "Baby yau baka dawo da wuri ba" "Na dawo da wuri mana ina kasa ne" zare jikinta tayi daga nasa ta koma gefan gado ta zauna taja tagumi tana kallonsa "Dan kana wajan matarka shine ka manta dani, kaki ɗaga kirana?" "Reina ni na isa na ki ɗaga kiranki ina masallaci san nan" "Na yarda muje kaci abinci ko kaci a masallacin" dariya Musty yayi yaja hannunta suka fito falo, gaban danning ta tsaya taja masa kujera ya zauna kana ta buɗe babban plate dayake cike da samosa da meatpie ta ajje masa a gabansa kana ta ɗakko sassanyan lemun abarba dake ajje cikin frezar ta zuba a cup "Ha" Aimanah ta faɗa yako buɗe bakin ta ɗora masa cup a bakinsa "Sha" tafaɗa a shagwaɓe hannunsa ya ɗora saman nata data rike cup ɗin, lemun yake sha idanunsa na cikin nata, idanunsa kawai ka kalla zasu bayyana maka asirin zuciyarsa na zallar soyayyar daya kewa Aimanah, harya shanye lemun bata ɗauke cup ɗin daga bakinsa ba itama ta shagala da kallon sa, cup ɗin ta ajje ta ɗauki samosa tasa masa a baki, ya lumshe idanu haɗe da girgiza kai "reina daɗi sosai fa zan iya cewa ban taɓa cin samosa mai daɗi irin wannan ba, haka lemun nan yayi daɗi sosai madalla da kulawa" sosai Aimanah ta ciyar da shi bai ankare ba kawai yaga goma saura na dare, "Rufe idanunki" ruf ta rufe tana murmushi, hannu yasa ya zaro car key daga aljihunsa ya saka a hannunta "Buɗe" lokaci ɗaya ta buɗe idanun nata kan hannunta tsalle tayi ta makale Mustapha "Baby car key, wayyo ni daɗi" "Tukwici ne na daranki na farko" "Baby" tafaɗa tana sake makalkalesa "Nagode Allah yasaka da alkhairi ubangiji yakara buɗi mai albarka" "Amin reina, Allah kuma yasa daran farko na jefa kwallo a raga" rufe idanu tayi tareda boye kanta a kirjinsa "Rakani bakin kofa na koma kasa" ɓata fuska Aimana tayi ta damke key ɗin hannunta ta koma saman bed ta kwanta, binta yayi ya sumbaci goshinta kana ya sake sumbatan laɓɓanta "Asuba ta gari reina karki manda da addu'a, idanunta ne sukai rau rau alamar hawaye na gafda zubowa da sauri yabar ɗakin, bayason ganin zubar hawayanta, key yasawa kofa ta waje tareda karanta ayatulkursiyyu kafa uku a bakin kofa kana ya sauka, Sumayya ta cika tayi fam kamar ta fashe ko sallamar dayayi bata amsa ba harya zauna kusada ita "Ya dai maiya faru na ganki cikin damuwa?" "Iya zuwan ma dakayi bai isa ba saika haɗa da wani abin kalli agogo fa awa nawa ka kwashe a wajanta kazo kuma sai kamshin turaranta kake, "Ya ilahi nikam dai na shiga aljanna...✍🏻 07039793439 [2/13, 4:45 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na Ashirin da huɗu* Afusace Mustapha ya tashi daga kusa da Sumayya ya raɓa can gefe yai shirin kwanciya "Bazaka kulani ba kenan ga mahaukaciya na ihu ko" "Sumy ya isheki ki barni nayi barci na huta please" "Daman haka zakace ai, anriga da anci Amanata" "Sumy zan mareki wacce amanar taki naci? ki shiga taitaiyinki karki sake ɗaga min murya, akan Aimanah zan iya aikata komai, Anma ci amanar taki mai zakiyi akai?" kansa ya maida saman fulo ya kwanta ya rufe idanunsa yana karanto addu'ar kwanciya barci Aimana dakyar tasamu barci ɓarawo ya ɗauke ta wani azababban kishi ki nu kurkisan zuciyanta inta tina yanzu Mustapha nacan rungume da matarsa, da matsanancin ciwon kai ta tashi dakyar tayi sallar asuba ta koma ta kwanta wani barcin, ba ita ta farka ba sai goma saura na safe, brush kawai tayi ta faɗa kicin yunwa takeji sosai, indomie ta dafa data sha attaruhu da albasa tas ta cinye kana ta shiga wanka, yau gaba ɗaya kewar Ma takeji hakan yasa bayan ta fito daga wankan zama tayi gefan gado taja tagumi, nan Mustapha ya tarar da ita ɗaure da tawul hannunsa yasa ya janye tagumin datayi ya zauna kusa da ita "reina lafiyarki kalau kuwa?" "Baby Mah nakeson gani" tafaɗa a shagwaɓe kamar zata fashe da kuka "Ok karki min kuka anjima zamu fita da yamma saimu biya ta gidan" rungumesa tayi kana ta ce "Thank you baby" bayan fitar Mustapha a ɗakin barci ta kuma kwanciya haka nan yau takejinta haka haka kamar mara lafiya, bata tashi ba sai da akayi sallar azahar nan ma salla tayi ta shiga kicin jallop spaghatti tayi da taji kifi da alayyahu taci sosai har mamakin irin yawan taliyar data ci take, tana nan zaune taji ana kiran sallar la'asar nan bathroom na falon tayi wanka ta shiga ɗaki tai sallah, sannan ta shafe jikinta da cream, shuwariski lace ta ɗauki porple doguwar riga A shape tasa sai walwali lace ɗin yake, bata ɗaura ɗan kwalin ba ta zauna gaban madubi tana gyara fuskarta sosai tai kyau na ɗaukar hankali ta saka sarka tana kokarin sa ɗan kunne Musty ya shigo ɗakin, ta cikin madubi take kallon sa yanda ya tsaya a bayanta ɗan nesa kaɗan da ita, mirmushi sukewa juna tana ɗaura ɗan kwali taji ya kwanto a bayanta "Wash baby zaka karya ni, kanada nauyi fa" sake gyara kansa yayi a bayanta yana shakar kamshi turaranta harta gama ɗaura ɗan kwalin bai sani ba, juyowa tayi yai saurin faɗawa jikinta tayi baya luu zata faɗi da sauri ya ruko ta ganin yanda ta tsorata sai zare idanu take "Ke kalle ni sosai" Musty yafaɗa sanda yai tozali da fuskarta data sha ado, farr tayi da idamunta tana murmishi kana ta zaro idanu "Gashi na kalleka" dariya sukayi gaba ɗaya "Wai a haka zaki fita kinga kyan da kikayi kuwa?" "Sai yau ka taɓa ganin kyau na?" "Ni bance ba kawai dai kwalliyar da zaman gida ta dace nasaki gaba nayita kallonki" "Uhmm umum fa baby gidan Ammi zan shiga daga nan ka kaini wajan Mah na kwana acan" "Cab amma dai bakida lafiya ko? kinsan yau ina nan zaki ce zaki kwana a gidan Maa ba yau ba" "Ni ni nidai gaskiyya..." "Gaskiyya me zo mu wuce lokaci na kurewa bana son mukai mangariba" mayafi ta yafa saman lace ɗin ta zura plate shoe a kafarta suka jera zuwa kasa, Sumayya na zaune taga sakkowarsu hannunsu na cikin na juna suna magana kasa kasa, Musty ya tsaya Aimanah ta zare hannunta daga cikin nasa tayi gaba zata fita "Baby mu haɗu a wajan Ammi" "Bakiga Sumayya ba zaki tafi baku gaisa ba" juyowa tayi ta kalli Musty ta kalli Sumayya tai kamar zata cigaba da tafiya sai kuma ta juyo zuwa inda Sumayya ke zaune saman kujera tana rike da waya "Ina wuni" Aimanah tafaɗa bata jira abinda zatace ba ta juya "Ki jira ni karki fita" kam ta tsaya daga bakin kofa ta juya masu baya "Sumy mun fita da Aimah" "Adawo lafiya" haka tafaɗa ta mike daga wajan ta shige ɗakinta, Musty hannun Aimanah yaja suka fita, ta kofar baya suka bi suka shiga gidansu Mustaphan ɗakin Momy suka fara shiga suka gaisa, faran faran fuskarta suka gaisa cikin fara'a, daga nan ɗakin Amarya suka shiga bata nan sai Murjana ita kaɗai kwance saman tiles da alama batajin daɗi, ɗakin Ammi suka shiga daga karshe murna sosai tayi ganin Aimanah a kallo ɗaya inka mata zakasan tana cikin kwanciyar hankali tayi kiba sosai tai haske kamar ka taɓa jini ya fito, har kasa Aimanah ta tsugunna ta gaida Ammi, Ammi da kanta ta ɗora ta kan kujera suna gaisawa ko gaisuwar Mustapha bata amsa ba, tana nan da Aimanah dake rufe fuska ita nan bata yarda ba kunyar Ammi takeji, tunda akai bikinta da Mustapha yau ce rana ta farko da suka haɗu da Ammi shiyasa duk takejin nauyinta "Ammi kona fita ne ko gaisuwata fa baki amsa ba" "Au zauna Babban mutum naga ɗazun nan ma kazo mun gaisa ka barni naji da bakuwata" Ahmad ne ya fito daga ɗakinsa yasha ado idanunsa na kan agogon hannunsa hannu yabawa Mustapha sukayi musabaha kana ya kalli Aimanah "Yaya Aimana ina wuni" "Yaya kuma dan Allah ya Ahmad karka sake faɗar wannan abin kunyar" "Dole nafaɗa kinsan sawun giwa ya take na rakumi" "Ban karɓa ba kirani da Aimanah sak dan Allah" "Yayanmu ayi haka kuwa" Ahamad yafaɗa yana kallon Mustapha da idanunsa ke kan Aimanah dake shan yoghout mai sanyi da Ammi takawo mata, "Ayi yanda tace ɗin yafi" kai Ahmad ya rausaya batare dayace komai ba "Dogo ajje mu a Ibrahim tayo road" da murmushi a fuskar Ahmad ya ce "Kayi sabuwa kenan" "A'a ta madam ce" "Mu tafi Aimah"mikewa Aimana tayi bayan tasa tushu ta goge bakinta, sukayiwa Ammi sallama, Ammi rakiya ta masu har wajan motar Ahmad, Musty yabuɗewa Aimana back seat ta zauna ya rufe sannan ya shiga front seat ya zauna, Ahmad yatashi mota suka bar layin, jefi jefi Mustapha ke juyowa yana kallon Aimanah dake chat ita da Rumana duk kan shirye shiryan bikinta da Abbas, har suka karasa inda Ahmad zai ajje su, wajan saida motoci, motoci ne kala kala a wajan duk ruwan idon mutum idan yaje wajan saiya zaɓa, idanun Aimanah sauka yayi kan wata bakar benz sai ɗaukar idanu take a gefe take da alama an riga an gama maganar ta ta wani ce tanaga shiyasa aka sakaya ta a gefe, sabuwa ce dal ko ledarta ba'a ɓare ba, "Barka da zuwa Alhaji" "Barka dai Alhaji Salim ya kasuwa" "Alhamdulillah ga ajjiyarka can tun jiya nake saka ran zuwanka" "Ban shigo kano da wuri ba shiyasa ban sami zuwa ba, jiya a airport muka haɗu da Mudassir yabani key na motar, Aimah bani key ɗin jiya dana baki," hand bag ɗinta ta buɗe ta ɗakko key ɗin Allah ma yasa ta tawo dashi, jerawa sukayi Aimanah na biye dasu abaya har gaban motar gaba ɗaya daɗi ya mamaye zuciyar Aimanah ganin wannan motar da idanunta ya sauka akai itace tata, hannu Mustapha yabawa Salim sukayi masabaha Salim ya koma gefe, Mustapha ya saka key ya buɗe motar "Bisimillah reina ga motarki shiga da bisimillah" karɓan key ɗin tayi ta shiga motar ta mata key "Baby Thank you mota nan tayi sosai, Allah ya saka da alkhairi ya biya bukatu na alkhairi, ubangiji yasa mu a aljanna" "Amin" Alhaji Salim yakawo masa takardun motar waɗanda ke ɗauke da sunan Aimanah, Musty ya mikewa Aimanah takardun ya rufe mata murfin motar ya juya ya buɗe murfin ɗaya ɓangaran ya zauna a front seat, Aimanah tayi kwana suka fita daga wajan saida motocin, Ahankali take tukin bakinta yaki rufuwa dan murna, hira suke sosai har suka karasa gadon kaya, horn tayi mai gadin gidan ya leko yana ganin Aimanah jiki na rawa ya wangale mata get ta shiga, ko gama saita parking batayi ba ta fita a motan da gudu ta shiga gidan "Mah mah mah kina ina" da sauri Mus'af dake tsaye kofar kicin yana jiran Mah ta gama gasa masa kifi, wata ya juyo tana ganin Mus'ab ta karasa wajansa ta kankamesa tana dariya, Mah data jiyo muryar Aimanah kashe oven ɗin tayi ta fito daga kicin ɗin, Aimanah sakin Mus'af tayi taja hannun Mah tana faɗin "Mah zo kiga mota ta" bayanta mah tabi har zuwa gaban motar da Mustapha yagama rufe motar ya fito, "Masha Allah mota tayi kyau Allah ya tsare, Mustapha kai kuma Allah yakara buɗi mai albarka, sai dai inada magana da kai biyo ni ɗaki" Mah nagama faɗar haka tayi gaba abinta ta koma ciki, Mus'ab yaja hannun Aimanah suma suka koma cikin, Mustapha jiki sanyaye zuciya fal fargaba ya shiga ɗakin Mah, ɗakin ba bakon sa bane tun tuni ya saba shiga tun zamanin kuruciya amma yau sai yake jin wani iri gaba ɗaya yakasa sakewa, Mah dake tsaye jikin madubi ta juyo ta kallo Mustapha "Mota biyu ka siya ko ɗaya" ɗagowa yayi ya kalleta kana ya ce "ɗaya ce" "Sumayya fa kana ganin kayi adalci kuwa Mustapha? ban laminta ba kuma zan ɗauka ba, kai ɗana ne ba siriki naba dole zanso naga ka yi adalci a tsakanin matanka, ya kake gani idan labari yaje kunnan Sumayya kasaiwa Aimanah mota ita baka sai mata ba, ba adalci bane wannan adalci shine kayi masu komai tare, san samu ma iri ɗaya sabida ban banta kala na iya kawo hassada wannan tana ganin na waccan yafi kyau dan haka gobe ba sai jibi ba naji labarin kasaiwa Sumayya mota hakan zai faranta min" "Insha Allah Mah zanyi yanda kika ce, Nagode Allah yakara lafiya da nisan kwana mai albarka" "Amin tashi kaje Allah yamaku albarka" "Amin" yafaɗa jiki a sanyaye yana fitowa ya tarar da Mas'ud suka fita tare a motar Mas'ud basu suka dawo gidan ba sai bayan sallar insha, lokacin Aimanah na sashin Daddy tunda yadawo gidan suna tare, sosai yayi murna da ganin yanda Aimanah ta canza yayi farin cikin ganin yanda ta karɓi kaddararta take zaune da Mustapha lafiya, duk motsinta Albarka kawai take saka mata tareda mata addu'ar zuri'a ɗayyiba, anan gidan Mah suka ci abincin dare kowa na mamakin abincin da Aimanah taci, banda Mah daketa jefawa Aimanah sannu tana murmushi, Abbas zaune cikin office ɗinsa dake cikin barreck ɗinsu wayarsa yake kallo ganin kiran Rumana sam yakasa ɗaga kiran matukar tausayin yarinyar yake dan daga alamu ta kamu sosai da sonsa, shi har yanzu bazaice yana sonta ba haka bazaice baya sonta ba, shi yanzuma ba wata soyayya a gabansa auran nan zaiyi ne kawai sabida girma da mutumcin Aimanah dayake gani banda haka bayajin nan duniya zai aure yana kallo kiran ya katse bai ɗaga ba, bai kuma bi kiran ba har tsawon mintina yana jiran ko zata sake kira amma ba ta sake ba, jiki a sanyaye ya ɗauki wayar tasa yabi kiran Rumana wacce yai save da Wife "Barka da yamma sojana" "Barka dai Wife yakike ya gida ya shirye shiryen biki" "Gashi nan munata yi, daman Yaya Aimanah tace nakira ka naji mai zamuyi na shagalin biki?" "Rumy banda cikakkiyar lafiya, bazan iya halartar ko wanne event ba kuyi ku kaɗai kawai" "Kana nufin baza kazo ko ɗaya daga ciki ba?" "Bazan sami zuwa ba Rumy" "Shikenan nagode na kuma fasa auran tunda so kake ka nunawa duniya ba sona kake ba" katse kiran tayi, mikewa tsaye yayi yana zagaye a ɗakin kiran Ruma yasakeyi amma bata ɗaga ba daya takura da kira ma saita kashe wayar gaba ɗaya Tex ya mata ya ajje wayar Rumana ranta ɓace ta kalli Aimanah "Na rantse da Allah yaya bazan auri Abbas ba, nizai wulakanta nifa daman bawani sonsa nake ba, biyayya kawai nakeson yi maki", "Rumana kiyi hakuri zaku sasanta kuma zai zo duk wani event da zamuyi na maki wannan alkawarin" Rumana ta matso kusada Aimanah ta saka hannunta cikin Aimanah "Yaya bazan ɓoye maki ba inason Abbas tun kallon farko dana masa ranar bikin uncle Yunus na kamu da sonsa, yanda bikinku ya kasance yasa nafara mafarkin auran Abbas, sanda kika zo min da rokonki kan na aure sa nayi farin ciki sosai, sai dai daga baya na fara tunanin nakai kaina inda zan wulakanta bana gaban Abbas ko kaɗan, yau yadaɗa tabbatar min da haka" "Rumana na rantse maki zaki alfahari da auran Abbas, ki daure komai zai faru a yanzu daga kin shiga ne komai zai wuce kefa maca ce" Da kyar Aimanah ta lalaɓa Rumana ta yadda suka cigaba da shirye shiryan bikin, Daddy da Mah sune sukayiwa Rumana komai na kayan ɗaki a jigawa gidansu Abbas akayi mata jere, sosai aka sha shagalin biki dinner kawai akayi Abbas ma ya halarta washe gari aka ɗaura aure Anty Hasana bata zo ba can a Qatar tayi taronta itada Dr shiyasa Daddy shine komai shiya ɗaura mata aure karfe biyu aka tafi da Amarya Daddy yace karsu sake su kwana suna kai Amarya su juyo, har Aimanah akaje jigawa bayan sun sha rigima da Mistapha yace bazataje ba ta ce sai taje rigima sosai sukayi har gaban Ammi goyan baya tabawa Aimanah ba yanda musty yayi yanaji yana gani haka aka tafi jigawa da Aimanah, hannu biyu Hajiya Hafsatu ta karɓi su Mah abinci kala kala aka kawo masu saida sukayi sallar Insha suka baro jigawa Rumana nata kuka, har Abbas ya shigo tana zaune saman bed tana kuka...✍🏻 [2/13, 4:45 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na Ashirin da biyar* Abbas ya tsaya a kanta yama rasa mai zaice mata can dai ya zauna kan gadon yasa hannu ya buɗe mayafin data rufe fuskarta da shi, ido huɗu sukayi da sauri Abbas ya ɗauke ganinsa kana ahankali ya ce "Kiyi shuru Rumy ki daina kukan nan yana tadan hankali" Ai kamar wanda yace cigaba da kuka ta kuma rushewa da kuka "Kinga tashi kiyo alwala muyi sallah mu godewa Allah daya mana wannan ni'imar mu rokesa yabamu zaman lafiya da fahimtar juna mai ɗorewa da zuri'a ɗayyi ba" bata masa musu ba ta mike tashiga ban ɗakin dake cikin ɗakin tayo alwala ta fito, yana tsaye kan daddumar daya shimfiɗa binsa tayi sukai sallah raka'a biyu sosai yamasu addu'a kana ya fita zuwa kichin yadawo rike da plate da ya ajje a gabanta kallo ɗaya tayiwa plate ɗin ta kauda idanunta kaza ce dataji kayan haɗi sai tururi take da tashin kamshi, lemu ya zuba a cup ya mika mata karɓa tayi ba musu ta sha kaɗan, ahankali yake bata zallar tsokar naman kazan tana taunawa kamar mai cin magani bata wani ci dayawa ba ta ce "Na koshi" kallonta yayi da murmushi a fuskar sa "Baza dai kici dayawa ba sabida tsoro ko" dariya tayi ta mike ta koma gefan bed ta zauna, tana kallonsa yagama kwashe komai yamaida kicin yadawo sanye da farar jallabiya ya kwanta ɗan nesa da inda take kwance, baice mata kala ba haka itama batace masa ba, har barci yayi awon gaba da su, da asuba ita ta rigasa farkawa mamaki tayi ganinta a jikinsa ya zagaye ta da hannayansa ta shiga jikinsa sosai, hannunta tasa tana kokarin cire hannunsa daga jikinta taji yayi motsi, a kunnan ta yake magana a hankali "Asuba tayi ne?" bata iya magana ba sai kanta data ɗaga alamar e, tashi yayi zaune kafin ya sakko kasa ya mika mata hannu ta ɗora nata saman nashi ya mikar da ita, tare suka shiga bayi sukai alwala ya wuce masallaci ita kuma ta tada sallah anan ɗakinta saman dadduma, Abbas bai dawo ɗakin ba sai bayan bakwai na safe ya tarar Rumana harta koma barci nan saman daddumar ɗaukarta yayi ya maida ta kan gado, ta buɗe idanunta dasuka soma canza kala ta kallesa kana tace masa "Ina kwana" "Kin tashi lafiya ya kwanan bakunta" dariya tayi haɗeda runtse idanunta ganin ya cire jallabiyan jikinsa ya rage daga shi sai gajeran wando da farar singleti gadon yahawo yajawo ta jikinsa, bikinsa ya haɗe da nata yana aika mata da wasu sakonni masu wuyar ɗauka, safiyar wannan rana Abbas yamaida Rumana cikakkiyar mace, yasha kuka yakushi harda cizo, barci ne yayi gaba da ita, shi kuma ya mike ya shiga bayi ya tsarkake jikinsa yai wanka ya fita sai faman murmushi yake shi kaɗai, sashin hajiya ya shiga har bedeoom ɗinta ya tarar bata ɗakin ya shiga ɗakin Babansa inda yake zaton tana can nan ma ɗakin ba kowa, motsin daya jiyo a kicin yasa ya leka, Hajiyarsa ce tsaye tana aiki a kicin ɗin, babansa kuma na tsaye jikin gaban teble yana gyara attaruhu, dariyar dayayi yasa suka jiyo gaba ɗaya suna kallonsa baba ma dariyar yayi ya ce "Kamin dariya mana, fisabilillahi da girmana da shekaru na akawo ni kicin asani gyara attaruhu wai lalle sai anyiwa surukata girki harda ni" Abbas dariya yayi sosai harda rike ciki yana kallon hajiyarsa data sha mur, ya karasa gaban Babansa ya karɓi wukar hannunsa "Abbas fita ka koma ɗaki kayi barcinka barsa Allah dashi za'ayi girkin nan," "Hajiya da dai kun barshi basai ayo order ba da safan nan ki wahalar min da Baba" hajiya batace komai ba taci gaba da abinda take, Haka Babanma Abbas ya gaida su ya fita yana dariya, sanda ya koma ɗakin Rumana na zaune kan gado farkawarta kenan daga barci gaba ɗaya jikinta ciwo yake mata musamman ma kasanta wani raɗaɗin azaba take ji ko motsi ta kasa, kallo ɗaya ya mata ya shiga bathroom ya haɗa ruwa mai ɗumi yadawo cak yaɗauketa daga gadon bai direta ko ina ba sai cikin ruwan daya haɗa, wata karar azaba ta saki tana kokarin fitowa daga cikin ruwan "A'a Hubbi daure ki zauna zaki daina jin zafin yi hakuri kinji" yafaɗa a tausashe kamar mai shirin mata kuka "A'a Kalbie bazan iya ba zafi nakeji wayyo Allah Anty zan mutu" hannunsa duka biyun yasa ya riketa ganin tana kokarin futowa daga cikin ruwan, bai saketa ba saida ya tabbatar ruwan ya yi sanyi kana ya fito da ita daga ruwan yace "Yi wanka" juyawa yayi ya fita daga bathroom ɗin ya koma ɗaki ya zauna haɗe da yin tagumi, ya zubawa kofar bathroom ɗin idanun yana jiyo zubar ruwan datake wanka, kulawa ta musamman Abbas ke bawa Rumana satinsu ɗaya a jigawa suka koma Abuja, saiga Rumana a gidan Abbas gidan daya gama tsara yanda zaiyi rayuwa da Aimana, gaba ɗaya ya manta da Aimanah yanda yakejin Rumana yanzu bazaice ta wuce Aimanah a zuciyarsa ba amma kam sosai yakejinta a zuciya musamman yanda take da biyayya bata taɓa masa musu ba iya tsawon zamansu, tana da tsafta batada son jiki ga iya girki da kwalliya. Aimanah na kwance kan gado, yau gaba ɗaya batajin daɗi zazzaɓi take ji, Mustapha ya shigo ɗakin yatarar da ita kwance "reina har yanzu baki tashi daga kwanciyar nan ba" ido kawai ta zuba masa ta kasa ce masa komai, hannu yasa ya taɓa jikinta yaji zafi zau "reina bakida lafiya kizo na kaiki asibiti" "Baby nifa lafiyata kalau, ina dai jin yunwa jikina kuma ba kwari bazan iya dafawa ba" "Mai zaki ci to" "Dambun shinkafa mai zogale da gyaɗa" "Yanzu reina ina zan sami dambu dan Allah yanzu da ranar nan" turo baki tayi gaba kana ta juya masa baya ranta ɓace, dafe kai yayi shima baice mata komai ba yafita daga ɗakin, kai tsaye gidan Ammi ya shiga yayi sa'a dawowarta gidan kenan daga makaranta gaisawa sukayi yai tsaye ya kasa ce mata komai, shi kunyarta ma yakeji jiya haka Aimanah tasa ta mata awara yau kuma gashi tazo da mata maganar wai dambu "Yadai babban Mutum kazo kamin tsaye anan" shafa kansa yayi kana ya ce "Ammi reina ce da rigima wai dambu zata ci ni narasa wannan cin nata" mirmushi Ammi tayi kana ta ce "Badamuwa zan bawa Surayya ta kawo mata" Mustapha ya juya ya fita bayan yayi mata godiya sanda ya koma gida yatarar Aimanah har tayi barci, bai tasheta ya zauna gefanta yana kallon yanda take barci ta wani taɓe fuska kamar mai shirin kuka ta cuno baki gaba, sumbatar kumatunta yayi ya fita daga ɗakin, Sumayya ta gama shaka ganin yanda yaketa zuruftu wajan Aimanah amma bata ce komai ba zura masa idanu kawai tayi, Aimanah sosai taci dambun nan, yau kuma gaba ɗaya sai taji nan duniya ba abinda takeson jin kamshi sama da turaran Mustapha ɗakinsa ta shiga ta rinka shan shana kayan sa harta gaji ta kira wayarsa "Baby nidai kamshinka nakeson ji kadawo gida" "Nadawo kuma ni bana ma kusa munje gwarzo nida Mas'ud" "Baby kasan yanda nakeso naji kamshinka kuwa dan Allah kadawo" "Ok gamu nan a hanya zanzo yanzu" shuru tayi nan barci ya kuma yin gaba da ita, sai farkawa tayi taga Mustapha a kusa da ita, jikinsa ta shige tana jin kamshin turaransa "Baby ki yarda muje hospital na rantse bakida lafiya, abincin da kike ci yayi yawa ga yawan barci yau zaki iya kirga sau nawa kikai barci" tabuɗe baki zatai magana amai yazo mata hannu tasa ta danne bakinta da gudu ta shiga bathroom na cikin falon ta fara kwarara amai kamar zata amayar da yan hanjinta, sosai ta galabaita, Mustapha na tsaye gefanta sai sannu yake mata, taimaka mata yayi tai brush suka fito yana rike da ita, zubewa tayi saman tiles tana juyi rikeda cikinta "Wayyo Yayanmu zan mutu, wayyo cikina" gaba ɗaya hankalin Musty yatashi "Baby kinga abinda nake gaya maki ko, zo muje hospital a...kafin ya rufe bakinsa wani aman ya kuma zuwar mata, wayarsa ya ɗauka ya kira Ammi yagaya mata Aimanah ba lafiya, kayan jikin Aimanah data ɓata ya cire mata ya taimaka mata tai wanka Ammi da Momy suka shigo lokacin Aimanah na kwance kan doguwar kujera tana murkusu su "Mustapha mai kake jira baka ga yanda take ba akaita hospital" Ammi tafaɗa hankali tashe ganin idanun Aimanah sun canza kala "Ammi taki yarda cewa take na barta ta mutu a ɗakinta" "To biye mata zakayi" Momy tafaɗa "ɗakko mata hijab" Momy tasa mata ta ruko ta suka fita, hankali tashe Mustapha ke tuki jefi jefi yana juyowa yana kallon Aimanah daketa kukan wayyo cikinta kirjinta kanta duk ta tashi hankalinsa har suka karasa ɗaya daga cikin hospital ɗin dake zoo road, nan da nan likitoci sukayi kanta aka ɗaura mata drip sannan nurse ta ɗebi jininta zuwa lap, bayan mintuna aka dawo masu da sakamakon Aimanah na ɗauke da cikin sati biyar "Sati biyar" Mustapha ya maimaita yana dariya, Ammi tai kasa da kanta tana murmushi Momy na faɗin "Alhamdulillah masha Allah, Allah abin godiya ubangiji ya raba lafiya" "Amin" Mustapha yafaɗa a fili, Ammi ta ɗago ta kallesa "Bakada kunya Musty a fili kake amsawa da Amin" "Ammi taya zanki amsawa addu'a fa mai kyau Momy tayi" "Zoka ajjeni a gida tunda ga Momy nan mai zanyi anan" ta fita bayan tayiwa Aimanah sannu, Momy tabi bayanta suna magana, Mustapha ya matso kusa da gadon da Aimanah ke kwance ya sumbaci cikinta, murmushi tayi tana kallonsa "Daman wai duk cin nan Babynmu ne yaja" "Baby na ce dai taja, nifa mace nakeson haifa" "Ni kuma boy nakeso nasa masa sunan Daddyn daya haifa min mata ta" taɓe baki Aimanah tayi tace "Allah ya kiyaye ni mace zan haifa Saudat" dariya yayi yana kallonta "Zan maida Ammi gida maizan siyo maki a hanya" "Apple" tafaɗa tana kautar da kai gefe, dawowar Momy ɗakin yasa ya fita yana murmushi Murjana gaba ɗaya abin duniya ya isheta tun jiya dataje chemist suka mata test suka tabbatar mata tana ɗauke da juna biyu tayi kuka sosai daran jiya ita kaɗai a ɗaki tayi nadamar da bata taɓa irinta ba, yau kwanan amarya uku bata gari tayita kiran wayarta bata ma shiga bare ta ɗauka hakanne yasa yanzu Murjana ta shiga wajan Sumayya, Sumayya da damuwa take cin ranta tana ganin Murjana ta fashe da kuka "Murja ina cikin damuwa a gidan nan, son Mustapha zai kashe ni gaba ɗaya bana gabansa, kina gani kwanaki fa mota ya saiwa Aimanah benz ni kuma ya sai min da toyota, komai zaiyi sai nata yafi nawa haka ake hakane adalci Murja?" "Hmmm Anty Sumayya kenan ke ki godewa ma Allah da wannan ɗin ma, kefa kika kawo kanki kika raba masoya Allah yayi kuma da rabon zama a tsakani komai ya rushe daman ai zaki ga abinda yafi haka yayi maki da kauna ma da bai sake ki ba, nifa masifar danake ciki tafi wacce kike ciki cikine dani fa harna tsawon wata uku ban sani ba" karaf maganar a kunnan Mustapha wanda ya shigo basu sani ba, hankali tashe yayi kan Murja da duka bugunta yake ta ko'ina da kafarsa "Murja mu zaki wulakanta ki tozarta mu kibar mana abin faɗa gayamin wane ya maki ciki ki gayamin cikin waye a jikinki" ganin taki magana ya shake mata wuya, idanunta suka firfito waje Sumayya ganin idanun Murja sun canza launi hankalinta ya tashi ta fice daga wajan da gudu ta nufi can cikin gidansu Mustapha, Murjana da taji azabar shaka ta ce "Na na na Salim ne, salim ne yamin" haɗata yayi da bango ya ɗauke fuskarta da marin da azabarsa tasa saida taga wuta "Waye salim ɗan waye ina ne gidansu zaki magana ko saina zubar maki da hakora" hankali tashe Ammi da yaya Ahmad suka shigo da kyar yah Ahmad ya iya ɓanɓare hannun Mustapha daga jikin murjana "Mustapha bakada hankali ne mai Murja ta maka har haka dazaka mata irin wannan dukan na fitar hankali" "Ammi ci ci cikene fa Murja, Murja ta cucemu ta ɓata mana suna" Musty fashewa yayi da kuka kamar wata mace yabar Ammi da Ahmad ba buɗaɗɗan baki, afusace Amarya da dawowarta kenan daga yawonta taga shugowar Sumayya hankali ta she kamar bazata shigo gidan Sumayyan ba sai kuma ta biyo baya taji maike faruwa, ganin Murja zaune kasan tiles tana numfashi ya kuma fusata ta ta karasa gaban Murjan tana tambayarta mai aka mata "Mama Murja fa cike ne da ita" Sumayya dake can gefe rakaɓe ta faɗa tana kallon maman tasu "Dan tana da ciki shine mai, a wannan zamanin ai ciki ba wata damuwa bace asibitocin da ake zubad da ciki ai yawa ne da su a garin nan" wasuma watan nin au nawa da aure ko ɓatan wata matansu basu taɓa yi ba shine sabida hassada yata na ɗauke da ciki zaku tara mata mutane, Ammi juyawa tayi tabar gidan ta koma sashinta, "Amarya kinsan mai kike faɗa kuwa yarki ce fa keda cikin shege" Ahmad yafaɗa cikeda mamakin maganganun amarya "Sai me Ahmad, abin kunya ai ba a kanta aka fara ba" Mustapha juyawa yayi ya haye samansa, Ahmad ya fice, Amarya ta ruko Murja suka fita suma, Sumayya kuka ta zauna tayi sosai na bakin cikin abinda yasami yar uwarta, labarin cikin nan dayaje kun nan Alhaji kamal har suma sai da yayi sabida tashin hankali, Murja tarinka kuka kamar ranta zai fita, tun tana basu Mustapha hauci har tadawo tana basu tausayi Alhaji Kamal sanda ya dawo hayya cinsa kasa magana yayi sai hawaye kawai dake bin kuncinsa tsawon lokaci Murja na gabansa tana kuka saida ya ɗaga kai ya kalleta kawai, Mustapha dake zaune a wajan tareda Ahmad, Musty yabata umarnin ta fita a ɗakin, fita tayi tana waiwayowa tana kallon baban nata "Abba kayi hakuri mai faruwa ta riga ta faru kasa karka furta kalma mara daɗi akanta idan bazaka saka mata albarka ba kayi shuru kar kace komai Abba" Mustapha yafaɗi haka jiki a sanyaye "Sakaci nane Mustapha laifin komai a kaina yake na ɗauki kaddara" "Baba bakada laifin komai kwaɗayinta itada mahaifiyarta shiya jawo komai, ta gaya min duk abinda yafaru dama wanda yamata cikin, zan neme sa muyi magana inyaso inta haihu sai ayi maganar auransu da ita suje su raini yaron" "Hakan yayi Allah ya sauketa lafiya" "Amin" suka amsa gaba ɗaya, Amarya na zaune a ɗakinta gaba ɗaya abin duniya ya dameta ko kaɗan batai farin ciki da samun cikin nan na murja ba a wannan kadamin data hango wani Alhaji daya mato kan Murja ɗin sanda ya ga hotonta a wayarta yace da gaske yana sonta da aure Alhajin ɗan siyasa ne, abokin mijin Hanne ne matar ta rasu yanada yara biyar, sosai tayiwa Murja sha'awar auransa musamman ganin yanada kuɗi kuma abin hannunsa bai dame saba hannunsa a sake yake, "Murja cikin nan na waye?" "Ance min cikin watansa uku a lissafina ciki na Salim ne shine wanda mukai ma'amala watanni uku da suka wuce" "Kiramin wayarsa muyi magana" kiran wayar tayi Salim ya ɗaga bayan sun gaisa da Amarya ta masa bayanin cikin dake jikin Murjana, wata dariya yayi ta shaki yai kana yai fito ya ce "Mama mama kenan ciki kuma ki tambayeta in zamuyi harka bana bata kwaya tana sha, kwayar hana ɗaukar ciki ita kullum nake bata tadai nemi uban ɗanta acan bariki badai ni ba" Amarya katse kiran tayi tana kallon Murja "Kindai ji abinda yace ko" "Naji daga farkon tarayyarmu inya bani kwayar ina ca amma daga baya sai nake kin sha sai na masa wayo na zubar" "Yanzu ai kinga wayo, tashi zakiyi muje a zubar da cikin nan bazaki bar min abin kunya ba cikin kishiyoyi" "Mama zubarwa kuma, dan Allah kibar min cikin nan inason abinda zan haifa na yarda ko katsina ne ki kaini na haihu acan" "Bazan kaiki ba na rantse da Allah sai kinzo munje an zubar da cikin nan" Murja ba yanda ta iya tabi Amarya suka sami wani asibiti anan aka birge cikin Murja wanda garin haka mahaifarta tasami matsala tanaji tana gani aka cire mata mahaifa yazamo itada haihuwa har abada" kuka take sosai da kuma istigifari tana rokon Allah ya yafe mata zunubanta, sanda Alhaji Kamal yaji labarin anzubar da cikin Murja kuma amarya ce taja nan take ya rubuta mata takardar saki uku yabata yace tabar masa gida bashi ba ita, Murja kuma ya bata sati ɗaya tak ta fito da miji yamata aure ko tabar masa gidansa tabi Amarya, Amarya ko gizo batayi ba dan ita a nata haukan taimakonta yayi yanzu ne zata fantama ta more dasu Hajiya Hanne, kai tsaye ma gidan Hanne ta maida komai nata sashi guda Hanne ta bata aka fara haɗa ta da mata suna holewa........😰 [2/13, 4:45 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na Ashirin da shida* Murjana gaba ɗaya duniya tayi mata zafi ta rasa wanda zata kawo har gashi yau saura kwana biyu wa'adin da Abba yabata ya cika, har Salim ta kira kan maganar auran zaki da cin mutumci shiya biyo baya, yau harta kwanta barci ta tina da Alhaji Jamilu da sauri ta cire lambarsa daga black list data saka sa bugun farko yaɗaga jiki na rawa ya ce "Murja nayi kewarki kwana dayawa sau uku ina zuwa kofar gidanku nayita zama amma bana ganin gilmawarki yanzu ina zamu haɗu?" "Alhaji kana sona zaka aure ni?" "So! sosaima kuwa nake sonki Murja, aure kuma ko yanzu kika ce na fito zanzo ga iyayanki" Numfashi Murja ta sauke kana ta ce "Ok kazo wajan mahaifina kuyi magana" "Nayi matukar farin ciki Murja Allah yabamu zaman lafiya amma dai kinsan sai kinyi istibira'i ko" "Na riga da nayi free" "Ok ki gayawa Abba gobe zanzo mu gana" "Allah ya kaimu" tafaɗa kana ta kashe wayar ta, "Aimana yanzu in kika bini yaya zanyi da Sumayya?" "Ni mai yayi ruwana da wata aba Sumayya ni mafita ta kawai nake nema, inka tafi kabarni yaya zanyi, ina zanji kamshinka nidai Allah binka zanyi" tafaɗa tana dire kafafu irin na shagwaɓaɓɓun yara, dariya yayi yana kallon yanda take kamar wata karamar yarinya, rigima da shagwaɓar Aimanah suna kara narkar da shi a kogin sonta "Ok dariya ma kake min ko, nidai a zubar da cikin nan tunda ai shine yajamin nakeson kamshin turaranka" "A'a reina kar ayiwa boy ɗina sharri fisabilillahi kwalba nawa ta turarena na ajje maki amma sai kice ke ba shiba na jikina kike so kawai dai nagano wayon so ake ayita zama a jikina" "Allah ba haka bane" tafaɗa tana faɗawa kan gado haɗe da fashewa da kuka, zama yayi kusada ita ya ɗagota ya haɗata da jikinsa yana kallon fuskarta kana yasa hannu yana goge mata hawaye "Kinga zaki ɓata min kyakkyawar fuskar nan taki nifa wasa nake maki, tashi ki haɗa kayanki jirgin yamma zamubi motarki da kayan nayi magana da Anty Halima driver ɗinsu zai tafi da su can legos inya kai sai ya biyo jirgi yadawo" tsalle tayi ta ɗane Musty tana ihun murna "Nikam Aimah zanga randa zaki girma" hara ta masa irinta masoya batace komai ba taci gaba da abinda take, fita yayi zuwa kasa wajan Sumayya Tana tsaye a ɗakin nata rike da waya suna magana da Amarya, shigowar Mustapha ɗakin yasa ta katse kiran tayi zuru tana kallonsa, zama yayi gefan gado ya nuna mata kusada shi ya ce "Sumy zoki zauna muyi magana" ba musu ta zauna inda yace ɗin, jimm yayi na ɗan lokaci har saida ta ɗago kanta ta kallesa taga shima ita yake kallo kasa tayi da kanta tana murmushi "Sumy kiyi hakuri da abinda zan faɗa ki fahimceni please" "Ina jinka" tafaɗa tana wasa da zoban hannunta "Zan tafi da Aimanah legos" da sauri ta ɗago ta kallesa sai kuma tayi kasa da kanta hawaye masu ɗimi suka biyo kuncinta "Shi yasa nace ki fahimceni Aimanah nada juna biyu, tunda ta sami cikin nan take son kamshin turare na, na ajje mata su dayawa amma sai tace na jikina take so yau ranar komawata legos ta tubure saita bini na rasa yanda zanyi da ita shiyasa nazo na roki kimin alfarma natafi da ita" "In naki yin alfarma fa?" "Dole ta zauna ai bazan shiga hakkin ki ba" "Hakki kuma na nawa Musty, ca nake nan kasai mata motar sama da miliyan talatin ni kuma kasaimin wacce bata kai miliyan goma ba" "Sumy kibar maganar motar nan, kyauta ce na mata tun tuni na kudurce a zuciyata zan mata wannan kyautar tun kafin ki shigo rayuwarmu, Sumy bazan ɓoye maki ba kin rigada kin sani Aimanah itace jini da tsokata itace bugun numfashi na karki soma kwatanta kanki da ita ina matukar iya bakin kokari na na kamanta adalci a tsakanin ku shiyasa kema na sai maki mota" tabe baki tayi ta tashi zata fita a ɗakin sai da takai bakin kofa sannan ta juyo ta kallesa "Na amince ku sauka lafiya" fita tayi daga ɗakin ta faɗa ɗakinta ta fashe da kuka, tabbas ayau basai gobe ba zata barwa Mustapha gidan sa bazata zauna kishi ya kasheta ba, to in kuma nabar gidan yasakeni ina zan zauna gidan mahaifina ba daɗi Mama tabar gidansu Mustapha ina zan kama tabbas dole na zauna a ɗakin mijina in yaso na nemi mafita kawai, ko Mama zanyiwa magana mu koma wajan tsito a farraka tsakaninsu kai ai kuma komai daɗewa asiri zai karye ga zunibi ga ba biyan bikata, ita kaɗai take ta zancan zuci har barci yayi gaba da ita tanata barci Mustapha suka tafi bata sani ba saida ta tashi a barci taga massages na Mustapha yana sanar mata sun wuce yazo suyi sallama ya tarar tana barci in sun sauka zai kirata a waya Rayuwa mai daɗi da kwanciyar hankali Aimanah keyi a legos tayi kiba ta kara yin fresh, kullum suna tareda Musty daga yadawo daga office baya kuma fita ko ina yana gida tare da Aimanah kulawa ta misamman yake bata yana, duk friday yake zuwa kano yayiwa Sumayya kwana biyu ya koma legos, Aimanah ta tsaye a kicin tana soya irish Mustapha ya shigo kicin, rungumeta yayi ya zagaye ta da hannunsa ɗaya ɗayan kuma yana shafa cikinta Reina yakamata ki rinka samun hutu fa tun asuba kina nan kina fama nace zan samo maki mai aiki kinki yarda" "Allah ya kiyaye baby inban kula da kai wazanyiwa ni bana bukatar wata mai aiki kawai ta kwace min kai" dariya Musty yayi haɗi da kwantar da kansa a bayanta yana lumshe idanuwansa "Reina zuciyata taki ce ke ɗaya ko bake a duniyar nan bana jin zan so wata bayan ke, ina sonki ina kaunarki! zuciya da ruhi duka na begenki hmmm reina baki yayi kaɗan ya iya bayyana kalar son danake maki ki kalli cikin idaniya su kaɗai sun isa su bayyana maki kalar so da kaunar danake maki, ko yaushe in ina tare dake ji nake kamar nan duniya gaba ɗaya babu sauran kowa daga ni sai ke Aimah I love you" "Love you tuch baby" tafaɗa tareda sumbatar hannunsa, "Kawo na karasa kije ki huta bari zan haɗo komai" "A'a baby kabarni na karasa ladana" "Nima ki bari na sami ladan, kije kawai bana son musu Aimah" hannunta tasa ta kunna famfon sink ta wanke hannunta ta fita, tana zuwa wanka ta faɗa ta shirya cikin farin wando dogo da karamar riga black colour ta ɗaure gashinta waje ɗaya bata saka hula ba ta fito falo tana danna wayarta, ya gama haɗa komai yana zaune a danning area yana amsa waya, kujerar kusa da tasa taja ta zauna tana kallon yanda yake dariya da alama ko da wa yake waya wayar na masa daɗi "Aboki bazaka gane bane abar maganar nan sai anyi bikinku da Surry zaka bani labari" tana jin haka ta gano da yaya Mas'ud yake waya, bataji mai yaya Mas'ud ɗin yace ba taji Musty na faɗin "Kaga gimbiyya na kusa bazaka cinye mata sauran lokacinta ba in na shigo kano ma karasa maganar amma dai nace ka zaɓi India kasar nada daɗin zama" bai jira abinda Mas'ud zai ce ba ya katse kiran, yaja plate yana zuba mata soyayyan irish ya mika mata gabanta tea ya haɗa mata yasa tea spoon cikin mug ɗin ya ce "Ha na baki a baki" "Zan iya jira ka bani kuwa nifa yunwa nakeji sosai" ɓata fuska yayi yana mata hararan masoya "Nidai saina baki Allah" yafaɗa a shagwaɓe haɗi da ɓata fuska "To naji gashi na buɗe bakin" Irish ɗin ya ɗiba ya zuba mata a baki ta soma ci a hankali, saida ya tabbatar ta koshi kana ya kyaleta "Baby nima tsaya na baka" zama ya gyara ta ciyar dashi cikeda kauna, har wajan mota ta masa rakiya tanata masa shagwaɓa harya kusa makara yatafi tana ɗaga masa hannu, sai da get man ya rufe get san nan ta koma ciki, gyara ko ina tayi ta sannan ta shiga kicin ta tarar ya wanke kayan da sukai amfani da shi, ta wanke plate da Mug ɗin da sukai amfani dasu ta wuce bedroom ta kwanta, bata tashi ba sai azahar sallah tayi tai wanka ta zauna suna chat da Rumana datake bata labarin rayuwar da suke itada Abbas tana mata godiya bisa zaɓin data mata, ganin biyu da rabi har tayi yasa ta mata sallama ta wuce kicin, wake ta ɗora a electry kana ta ɗora shinkafa kan gas ta ɗebo kayan miya ta wanke ta saka hand clove ta gyara kayan miyan ta cire dattinsu ta sake wanke su sosai da gashiri kana ta markaɗa su a blandar kafin la'asar ta gama haɗa lafiyaryar shinkafa da wake da miyar dake ta tashin kamshi ta yanka salad tumatir cucumber da albasa har green pepe ta zuba haɗaɗɗiyar kula ta kawo su dannin area ta ajje, salla taje tayi bayan ta idar azkhar na maraice tayi ta ɗau wayarta ta kira Mustapha, bugun farko yai pickin call ɗin "Barka da aiki Rayuwata" "Barka dai habibiya" "Baby inajin yunwa fa baka dawo ba har yanzu" shafa kansa yayi yana murmushi yayinda kujerar dayake kai ke juyawa da shi, sai wani kumshe idanu yake da gani wayar na masa daɗi "Beb kici kawai, ayyuka sun rikeni Aliyu baya nan ya haɗamin aikin office ɗinsa da nawa gaba ɗaya ni nake yi inaga sai mangari ba zan da wo" "To abincin fa? haka zakayita zama bakayi lonch ba gaskiyya bazan laminta ba, sai yunwa ta kama min kai," " zan.." A'a Baby karka gayamin zaka ci abincin waje, Allah bazan yarda ba, ko nazo na kawo maka nan" "A'a bari na turo driven mu na office ya karɓar min ki bawa Joseph in yazo sai ya basa" dariya Aimanah tayi tana mamakin kishin Mustapha "And kisa hijab kuma basai kin masa magana ba zan masa waya" "Baby" "Uhmm bebyn baby yane" . "I love you" kissing wayar tayi kana ta katse kiran, tayi kamar yanda ya ce, bai dawo gidan ba kuwa sai gabda sallar insha, wanka kurum yayi ya fita masallaci dake nan kusada gidan, wajan takwas da rabi ya shigo gidan ya tarar tana zaune a danning area, can ya isketa yana mata sannu, soyayyar taliyar da tayi wadda taji kayan lambu ta zuba masu a plate suna ci a hankali suna hira jefi jefi A kano tuni aka ɗaura auran Murjana da Alhaji Jamil ta tare a gidansa da yake tare da matarsa anan tarauni , sam bata sami matsala da matar saba mace ce yar ba ruwana aikinta kawai tasa a gaba sai dai ta kula tana yawan tara mata a sashinta datayiwa Alhaji Jamil magana yace ai tana business ne shiyasa, ganin bata shiga sabgarta itama saita kama kanta kusan ma ba zaman kasar suke da ba kullum suna tafe itada Alhaji Jameel data zamo masa jela. *Gidan Abbas* Ruma na kwance lamo kan kujera yayinda Abbas ke zaune kan carfet yana aiki a laptop ɗinsa, jefi jefi yake kallon ta ganin yanda take juyi kan kujera "Rumy yane?" yafaɗa yana barin danna laptop ɗin dayake "Hayatie cikina ciwo wayyo ƴa'ƴan cikina zasu zubo" da sauri ya mike ya karasa kusa da ita ya ɗagota ya haɗata da jikinsa "Daman bakida lafiya baki gaya min ba mai yasa kika ɓoyemin" "Yanzu ne fa, yanzu naji cikina na ciwon wayyo zan mutu" tafaɗa tana juyi tareda wata mika, gaba ɗaya hankalinsa yata shi lambar nurse jamila dake cikin barreck ɗinsu yake kira amma bata shiga, da sauri ya mike ya ɗauki Rumana cak ganin idanunta sun kakkafe, yafita da ita yana kwalawa jakop direver ɗinsa kira da sauri jakop ya karaso inda uban gidan nasa ke kiran sa "Jakop maza ɗakko mota muje hospital Rumy ba lafiya" yafaɗi haka yana leka idanunta dayaga sun kafe waje ɗaya "Jakop" yafaɗa da karfi hankali tashe a bayan mota ya kwantar da ita yana tukin da hankasa, mahaukacin gudu yake bisa kwalta yanayi yana juyowa yana kallon Rumana dake kwance kamar gawa....✍🏻 [2/13, 4:45 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na Ashirin da bakwai* *Wannan page ɗin gaba ɗayansa sadaukarwa ne ga yan Aimanah real fans group 2 comment ɗinku na matakur sani nishaɗi ina godiya da kulawa mutane na* Hankali tashe likitoci suka karɓi Rumana akai emargency da ita, tsananin tashin hankalin da Abbas ke ciki yasa ko gabansa baya iya gani, Jakop ya taimaka masa ya zauna a recepsion yadafa kansa yayinda shi Jakop ɗin ke zarya tsakanin inda Abbas yake da inda aka kwantar da Rumana "Ina yan uwan Rumana Mahmud" da sauri Abbas ya mike tsaye yabi likitan zuwa office ɗinsa, kujera ya nunawa Abbas dake tsaye kikam a kansa, ba musu ya zauna zuciyarsa na dukan uku uku "Sorry matarka tayi ɓarin cikin wata biyu" a razane ya ɗago idanunsa yana kallon likitan, hawaye suka zubo daga idanunsa shikenan sun rasa wannan cikin da suka kwallafa rai a kansa, ya Hajiya zataji idan taji wannan labarin mai tada hankali "Kayi hakuri mahaifar Rumana nada rauni koda ta sake samun wani cikin banajin zai zauna sai dai zamu ɗorata kan magani sannan zata cigaba da zuwa ganin likita duk bayan sati biyu" Abbas kansa kawai ya ɗaga alamar yaji, Dr ya mika masa takarda ya ce "Ga wannan asiyo waɗan nan magungunan da allurai" karɓa Abbas yayi ya fita, Jakop yabawa takardar shi kuma ya shiga ɗakin da aka kai Rumana, tana kwance samɓal saman gado kamar gawa ko motsi batayi a kallo ɗaya daya mata yaga ta rame sosai kamar wacce ta shekara tana cuta, hawayan idanunsa ya share ya sumbaci kuncinta ya fita daga ɗakin, recepsion ya koma ya kira wayar hajiyarsa bugu ɗaya a na biyu ta ɗaga "Soja mazan fama barka da yamma ya surukata" "Hajiya" zuciyarsa ce tai wani irin rauni ya na shashshekar kuka ya ce "Rumy tayi ɓari" "Ɓari! innalillahi wa'inna ilaihir raji'un yanzu tana ina?" "Muna hospital" "Kamata sannu zan biyo jirgi na tawo na kula da ita" "Hajiya basai kinzo ba zan kula da komai" "Malam Abbas kabari kawai nazo, kaga yanayin aikin ka yanzu ma ana iya kiranka batada kowa a Abuja wazai zauna da ita kabarni kawai nazo" "Shikenan Hajiya Allah yakawo ki lafiya" Abbaa komawa ɗakin yayi yaja kujera ya zauna kusada gadon hannunta na cikin nasa, motsi tafara yi kana ta buɗe idanunta, lemar dataji a kasanta yasa ta kankame hannun Abbas dake cikin nata "Hayatie maiya same ni mai ya sami cikina?" "Ba abinda ya sameki Rumy kina lafiya, haka cikin ki ma yana lafiya" "A'a Hayatie ka faɗa min gaskiyya jini ne fa yake bina" "Kinyi ɓari ne" Abbas yafaɗa a sanyaye "Cikina ta zube wayyo Allah na" "Kiyi hakuri Rumy kwana nawa ne zamu sami wani dan Allah karki saka damuwa a ranki Allah shiya bamu wannan lokacin da bamu zata ba ko tsammani, shi zai kuma bamu wani kilama ki mana tagwaye" yakarasa faɗa yana murmushin karfin hali, Rumana maida kanta tayi ta kwantar haɗeda runtse idanu hawaye na zubowa daga idanunta, Hajiyar Abbas a ranar tazo ita taci gaba da kulawa da Rumana. *Musty Home* "Baby danna min kafar nan sosai zugi takemin bakaji azaba ba" Mustapha dake matsa mata kafa kara himma yayi tareda aika mata sannu akai akai tausayi take basa sosai ganin yanda ta kumbura musamman kafafunta da suka tasa cikinta mai wata huɗu inka kallesa zakace yakai watanni bakwai sabida girmansa, wayarta dake kusa da shi ce tayi kara alamar kira ya shigo hannu yasa ya ɗauka ya mika mata cikeda ɗoki ta ɗaga ganin Rumana ce ke kiranta, "Hasbunallahu wani'imal wakil" Aimana ta faɗa a razane tareda sakin wayar tata ta faɗa kan cinyarta, a razane Musty ya ɗago ya kalli Aimanah dake kokarin mikewa tsaye "Ke maine wai nutsu Aimah" "Baby Rumana ce a asibiti tayi ɓari" tsaki yaja yana cigaba da abinda yake a fusace ya ce "Shine kika ruɗe haka, dan tayi ɓari Allah zai basu wani ai" saroro tayi tana kallonsa cikeda mamaki "Baby Rumana fa!" "Rumana maizan mata fatan samun lafiya kawai zan mata" fusge kafarta tayi ta mike "Nidai Abujan zan tafi naga lafiyar yar uwata" "Kiga lafiyar yar uwarki ko ki gano masoyinki" "Mustapha" Aimana ta faɗa cikeda mamakin maganarsa, bai ɗago ya kalleta ba saima danna wayarsa daya fara yi ganin bai kulata ba yasa taci gaba da magana "Nidai wallahi sai naje na duba Rumana yaufa kwananta huɗu a hospital ta kirani ta gayamin sannan kace bazani ba Allah sai naje naga yar uwata" kanzil baice mata ba saima tashi da yayi yabar mata gidan, bai dawo gidan ba sai batan sallar insha abinda bai taɓa mata ba matsawar yana gari baya fita ko ina ko wani uzirin ne ya kamasa na fita tare suke zuwa ko ina ne, a ɗakinsa ta kwanta ya shigo yana ganinta baice mata komai ba yai shirin barci ya kwanta can karshan gado nesa da ita sosai, ganin haka saita juya baya, washe gari kafin ta tashi yagama haɗa break yaci nashi yabar mata nata nan saman danning ya wuce office "Kam bala'i" Aimana ta faɗa sanda taga abinda yayi agidan kicin ta wuce ta haɗa abinda takeso taci ta ajje sauran, saida ta fuskanci lokacin dawowarsa yayi ta koma ɗaki ta kwanta lamo kamar mara lafiya, tana ganinsa ya shigo ɗakin da sallama kasa kasa, suit ɗinsa ya cire ya ɗaura tawul ya wuce bathroom bai kalli ko inda take ba, yana fitowa daga wanka ya ganta zaune kan gado tana kuka kasa kasa ba karamin juriya yayi ba ganin bai kulata ba, jin kukan yake har cikin ransa, ta gefan idanunsa yake kallonta yayin da yayi kamar baisan tana yi ba, wayarta ta ɗauka ta kiran layin Ammi "Ammi Mustapha zai kashe ni daga nace zanje na duba Rumana shikenan yaɗau fushi dani ya daina kulani ya daina cin abinci na yama daina kwana a ɗakin danake" murmushin gefan baki yayi yana satar kallonta ganin yanda take haɗa masa karya a gabansa ko kunyarsa bata ji "Shi mai babban sunan yamaki haka, cab bari na kirasa naji dalilin da zaiwa yar Ammi haka kuma ki soma shiri gobe zaki gano yar uwarki" kwalo tayiwa Mustapha a zatonta baya ganinta, Musty yana ganin kiran Ammi yaki ɗagawa saima barin ɗakin dayayi da wayar a hannunsa, saida ya futa compound na gidan kana yabi kiran Ammi daya katse, Aimana batasan ya sukayi ba taga dai yadawo ɗakin ya kwanta baice mata komai ba, sa da tabari yayi nisa a barci ta tashi tsakiyar gado ta zauna tana faman kukan shagwaɓa "Aimanah baza ki barni nayi barci ba ko?" "Ba kaine ba kadaina min magana" tafaɗa cikin kuka, dafe kansa yayi gamida zuba mata idanu kana ganin yanda take kukan kasan na zallar shagwaɓa ne, matsowa yayi kusada ita yasata a jikinsa yana buga bayanta a hankali da hannunsa "Is ok ya isa Reina kece rigimar ki tayi yawa a wannan halin da kike ciki kice wani zakiyi tafi" "Naga a jirgi zanje kuma ai ba kwana zanyi ba randa naje ranar zan dawo bafa nisa legos zuwa Abuja" "Hmmm" kawai yace ya kwantar da ita haɗida sata a jikinsa yana share mata hawaye har sukai barci a haka, shiya rigata ta shi yauma yayi abinda zaiyi ya fice sai text messages dayai mata na fatan ta taahi lafiya ya kuma sanar da ita ta shirya zasubi jirgin karfe biyu zuwa Abuja, murna tayi sosai sanda taga sakon cikin lokaci kankani ta gama komai, Aimana maca ce mai tsabta da iya girki ga uwa uba iya ado da kwalliya, ko kafin Musty yadawo tagama komai harta shirya cikin doguwar riga yar dubai tayi matukar kyau, sanda yadawo wanka yayi suka ci abinci ya fita masallaci yai sallah itama tayi nan cikin gidanta yana dawowa suka wuce airport yariga da yasaba indai zaiyi tafiya nan cikin airport ɗin yake varin motarsa inya dawo ya ɗauki abarsa, lafiya suka sauka Abuja duk ɗoki da son ganin Rumana da Aimanah take haɗiye sa tayi dan tunda suka sauka a Airport na Abuja Mustapha ke cika yana batsewa, wani haɗaɗɗan hotal Mustapha ya kama masu can suka sauka a recepsion ya karɓi key na ɗakin ya wuce dan tun a office ɗinsa ya gama komai ta online shiyasa key kawai suka basa anriga da an gaya masa number ɗakin, suna shiga ɗakin Musty tafara rage kayan jikinsa ya rage daga shi sai singlate da gajeran wando ya haye gado yana faɗin wash "Amma yaya inace hospital ɗin zamuje" kanzil baice mata ba saima gyara kwanciya da yayi yana kallon agogo, ba yanda taso itama kwanciyar tayi nesa da shi ta cure waje guda a haka barci yayi gaba da ita, Kiraye kirayan sallar la'asar ya farkar da Mustapha daga barcin da yayi yaga yanda Aimanah ta cure waje ɗaya, da sauri ya gyara mata kwanciya ya lulluɓa mata blanket ya wuce bathroom yai wanka da alwala ya wuce masallacin dake nan cikin hotal ɗin, harya dawo rike da babbar leda a hannunsa bata tashiba shima bai tashetan ba sai wayarsa daya ɗauka yana dannawa, biyar da kwata Aimanah ta farka taga gari yafara duhu addu'ar tashi daga barci tafara kana ta tashi zaune "Sannu kin tashi" gira kawai ta ɗaga masa ta mike ta shiga bayi tayi wanka da alwala, futowa tayi tana raba idanu "Yanzu kayan nan zan maida wai" da idanu ya nuna mata ledar dake ajje saman bedsite drowar buɗewa tayi dogayan riguna ne guda biyu yan maroco ja da baka sai manyan hijabai guda biyu, jar tasaka ta ɗaura karamin mayafin rigar a kanta ta saka hijab ɗin tai sallah, kafin ta idar taga yagama shiryawa cikin bakaken suit sak yafito a kalarsa ta ma'aikacin banki🤭tana azkhair ya zauna gefanta ya ajje likab a gabanta, dariya taso kwace mata amma sai ta shanye ta, ta shafa fatiha tana kallon sa shida likabin gabanta "Kisa muje hospital ɗin" "Inajin yunwa, kuma Allah bazan saka abin nan ba, ban taɓa sawa ba dan haka bazan koya yau ba" "Aimanah ki taimaki zuciyata ki sakaya min kyakkyawar fuskar nan taki" "Mustapha kar muyi haka dakai duka akan Abbas ne kake wannan abun, Abas Rumana yake aure, na tabbata a yanzu babu wani sauran abinda yayi saura tsakani na da shi, kai nakeso kaine abokin rayuwar da Allah ya zaɓa min koda baka raye nan duniya bana jin zai iya auran wani kisa a ranka ni taka ce har abada na roke ka ka rage kishin nan naka akan Abbas" Jikinsa ne yai sanyi da maganganun Aimanah hakan yasa yai shuru tareda komawa gefe ya kira a waya aka kawo masu abinci, basu sami fita ba sai bayan da sukai sallar mangari ba sannan suka fita zuwa hospital ɗin da Rumana take "Baby a ina kasami mota?" "Munyi magana da yah Mansur shiya saka aka kawo min" "Mutanan landon ana can" "Suna can kam ɗazu mukai magana da Mus'ab ma zai wuce Rasha acan zaiyi P h d" taɓe baki Aimanah tayi kana ta ce "Shikenan gida yazama sai Mah da Ma'aruf kowa yasa gabansa yabar kasar" "Wanda yasami dama ya dama Aimanah wannan kasar tamu sai dai addu'a kawai nima nafara tunanin komawa jordan can inda nafara aiki" "Amma badai dani ba" "Da Sumy" yafaɗa yana hararata sunata hira har suka karasa hospital ɗin [2/13, 4:45 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na Ashirin da takwas* Cikeda tausayawa Aimanah takewa Rumana sannu, tana rike da hannunta "Hajiya ina wuni" Aimanah tafaɗa tana kallon Hajiyar Abbas data fito daga bathroom, hajiyar Abbas ta rike baki cikeda mamaki fuskarta da murmushi "Wa idanuna ke gani kamar Aimanah mutanan legos, yar uwarki ta taso ki ko?" "Nice Hajiya yamai jikin" "Jiki da sauki gobe ma zasu sallame mu mu koma gida" Aimanah kan tayi magana aka turo kofa aka shigo Abbas nw shida Mustapha sai Ammi a bayansu "Lah Ammi daman kina nan" "A'a yanzu nazo Abbas ne ya ɗakko ni a airport ashe kunzo" Musty can gefe yasamu ya zauna saman farar kujera yana kallon Aimanah "Yaya Abbas ina wuni ya mai jikin" "Da sauki" Abbas yafaɗa idanunsa na kasa, Aimanah sun jima a hospital ɗin har tara saura, Mustapha yabawa Abbas hannu sukayi musabaha tareda fatan sauka lafiya, Aimanah tabi bayan Muatapha daya fita bayan tayi sallama da su Rumana, Aimanah da Mustapha kwanansu biyu a Abuja kana suka wuce kano inda aka fara bikin Surayya da Mas'ud, Aimanah bata wani sake sosai a bikin ba duk da dama ba wani shagali aka sha ba to ango yana india wajan karatu can za'a tura masa amaryarsa bayan an ɗaura aure, satin su Aimanah biyu a kano suka koma Abuja, Rumana sosai take samun kula ta musamman wajan Abbas, Hajiyar Abbas tunu ta koma jigawa vayan taga Rumana ta warware, sauri sauri Rumana ta shiga wanka ganin lokacin dawowar Abbas yayi akuwa tana bathroom ta jiyo karar tsayawar motocinsa, kafin ta fito harya shigo ɗakin sanye ta fito da tawul ɗaure a kugunta yayinda hannunta ke rike da ɗaya tana tsane gashin kanta "Wellcome sir" tafaɗa tana tsugunnawa a gabansa ta fara cire masa takalmin kafarsa duka biyun ta cire ta ajje su mazauninsu kana ta dawo ta fara rage masa kayan jikinsa, janta yayi sukayi baya suka faɗa saman gado suna dariya "Mar'atul saliha albushirinki" "Goro" tafaɗa da sauri "Gobe sassafe zaki sama sabuwar ɗaliba a jami'ar abuja" makale shi tayi sosai tana ihun murna "Hayatie da gaske dan Allah wayyo ni ina kasami takardu na" "Jaheed ya turomin da komai" "Naji daɗi sosai Hayatie nayi farin ciki yanda kake faranta min kaima Allah ya faranta maka fiye da haka" "Amin yafaɗa yana sumbatar ta" daga nan salo ya canza suka lula duniyar masoya🤭 Aimanah na vaje a falon tayi ɗai ɗai tana fidda numfashi yayinda Al'Mustapha ke zaune kusa da ita yana yanka kata Apple "wash" Aimanah tafaɗa cikeda raki "Sannu reina sannu kinji" "Baby na gaji da cikin nan gani nake ma kamar mutuwa zanyi" Aimanah ta karasa faɗa tana kuka, ya buɗi baki zaiyi magana wayarsa tayi kara alamar kira ya shigo, Ammi ce hakan yasa ya ɗaga cike da ladabi "Mustapha zan saɓa maka fa yaushe kadaina jin magana ta" Musty dafa kansa yayi a zuciyarsa yana faɗin wayyo ni "Ammi kiyi hakuri Aimanah tayi nauyi da yawa idan ta tawo kano a haka zata wahala" "Ni kuma nace ka kawo min ita yau zuwa gobe nabaka ka wucw wannan wa'adin zan saɓa maka" Ammi nagama faɗar haka ta katse kiran "Kamaida ni kanon in mutuwa ma zanyi na mutu cikin Ahali na" "Aimanh ba yanzu ba insha Allah sai kinga auran twince ɗinmu da jikokinsu" murmushin yake tayi tana jin mararta na kullewa, yayin da abinda ke cikinta yayi wani irin motsi "Ya Allah" Aimanah ta furta a hankali "Sannu" kawai yake aika mata, a washe garin ranar Mustapha ya maida Aimanah kano suna sauka Ammi taji labari tazo ta wuce da Aimanah gidanta tanata ma Mustapha masifa ganin yanda kafafunta suka kumbura, a daran ranar ta kaita hospital suka dubata sosai haɗeda mata hoton ciki inda suka sake tabbatar yan biyu ne a cikin Aimanah kamar yanda a asibitin da take awo a can legos suma suka faɗa, cikin wata takwas harda sati biyu, Mustapha kwanan sa biyu ya koma legos shida Sumayya cikeda kewar Aimanah, Rayuwa mai daɗi da kulawa Aimanah keyi a gidan Ammi sai abinda takeso take ci kullum sukam futa da dare suyi zagaye su dawo, Mustapha tunda yatafi sai da yayi kwana goma bai zo kano ba, yau yakasa jurewa ba shiri ya biyo jirgin karfe tara na dare, lokacin daya zo sai Aimanah ita kaɗai a ɗakin Ammi, Ammin bata nan tana wajan Abba, da sallama ya shigo bedeoom ɗin Ammin, Aimanah da barci yafara ɗibanta ta buɗe idaninta a hankali da sauri ta tashi zaune tana mistsika idanunta "Baby" tafaɗa da muryar barci "Bakiyi barci ba? ina Ammi?" "Yanzu ta shiga wajan Abba tace bazata jima ba taje basa tea" dariya Musty yayikan ya ce "Taje basa tea kawai dai ta tafi kula da mijinta ke kuma ta rabaki da naki mijin" "Oh Baby" "Gaskiyya fa nafaɗa" dariya tayi, ya zauna kusa da ita ya ruko hannunta "Nayi missing naki sosai reina" yafaɗa yana sumbatar hannun nata, dai dai nan Ammi ta shigo ɗakin da mamaki take kallon sa ta haɗe rai "Kai kuma maiya kawo ka da wannan daran?" "Ammi naji kewar Aimanah ne kawai ba biyo jirgi na ganta" taɓe baki tayi sannan ta juya ta fita daga ɗakin, Musty bayanta yabi yasawa kofar key yana murmushi, gadon ya hawo sosai yasa aimanah a jikinsa yana sauke ajjiyar zuciya a jere kamar wanda yayi gudu, Aimanah ma lamo tayi a jikinsa tsawon lokaci suna rungume da juna ganin time na ja yasa ya cire jikinsa daga nata ya fita daga ɗakin, Aimanah gyara kwanciyarta tayi tana jin kewar mijinta na shigarta, har tayi barci Ammi bata dawo ɗakin ba, sai da safe ta ganta kwance kisada ita, Musty bai shigo gidan ba sai da ya tabbatar Ammi ta tafi makaranta sannan ya shigo sashin Momy ya shiga ya tarar bata nan itama, daɗi yaji sosai hakan yasa ya shiga ɗakin Ammi cikeda karsashin son kaɗaicewa da Aimanah kofar sashin ya fara sakawa key bayan ya shiga haka yayiwa ta falo ma, Aimanah taso kin bashi haɗin kai tana nuna masa rashin dacewar abin a ɗakin Ammi, wasanni daya rinka mata yasa ta bada kai bori ya hau, sai dai suka nutsu kana kunya duk ta kama ta gani take kamar Ammi taga komai da kyar da taimakonsa ta gyara jikinta ya cire bedshet ɗin yasa a wash machine ya wanke ya shanya yana addu'ar Allah yasa ya bushe kafin Ammin tadawo, Aimanah kaɗan kaɗan tafara jin ciwon mara azatonta kaɗaicewa da sukai da Musty yakawo haka take ganin gaba kaɗan zata daina ji, maimakon ciwo yayi baya sai yayi gaba tun tana jurewa harta kasa ta kira lambar Ammi ta sanar mata abinda takeji, Ammi tace mata ta jirata gata nan tana hanya tama kusa shigowa anguwar, Musty na can gidansa yana barci, ko kafin Ammi ta karaso Aimanah tafara fita hayyacinta, tayi sa'a tare suka shigo gidan da Ya Ahmad hakan yasa tasa shi suka nufi hospital, wayar Musty Ammi ta kira tace ya ɗakko masu kaya a ɗakinta suna hospital ruɗewa tasa basuma taho da komai ba ance haihuwa ce, Aimanah na zagaye cikin Asibitin taga shigowar Mustapha ya ruɗe sosai, Aimanah tun tana iya zagayan harta gaji kar finta na neman karewa aka maidata ɗaki har sannan da likita ta dubata a 4 cm take, Musty na rike da hannun Aimanah duk yanda likitoci suka so yafita a ɗakin ki yayi ganin ba wata a ɗakin sai Aimanah kaɗai yasa suka barsa, idanunsa kaɗai zaka kalla kasan yanajin ciwon gaba ɗaya yadamu jiyake ina ma da dama da ya karɓi leboor ɗin nan Aimanah ta huta, Tun safiya Aimanah take abu ɗaya har mangariba bata haihu ba, Musty sallah kawai ke fitar da shi daga ɗakin har kuka ya yiwa Aimanah musamman yanzu data fara kuka tana neman yafiyar mutane tana faɗin mutuwa zatai, Nurse ɗin dake zaune gefansu ya kalla "Babu wani abu da za'a iya mata ne wai?" ya tambayeta cikeda damuwa "Babu, zata iya haihuwa da kanta yanzu tana 8 cm nan da ko yaushe zata iya haihuwa" kukan jaririn da sukaji ya karaɗe ɗakin yasa Musty faɗin "Alhamdulillah Allah abin godiya" da sauri likita dake office ɗinta ta fito ta karaso bakin gadon tana yiwa Aimanah sannu "Dr ɗaya ne yafaɗo akwai wani a cikin kuma da alama mahaifarsu ɗaya ce, Nurse Musty ta kalla "Matso ka rike wannan karkayi nisa" matsowa yayi ya karɓi jaririn dake faman tsan yara kuka ya rike idanunsa nakan Aimanah dake kiran sunan Allah ya share hawayan idanunsa yana sauke ajjiyar zuciya "Sannu Aimah" bata ko iya ɗaga kai ta kallesa ba, "Aimanah tsaya kar kiyi nishi" likitan ta faɗa tana danna mata ciki a hankali, kamar cirar kaya haka Aimanah taji sanda ta sake jin kukan wani jaririn ciwo ya tsaya cak Murmushi Musty yayi sai sannan ya kalli yaran, da Nurse ta matso ta zata yanke masu cibiya, wani gadon tayi daban da yaran Musty yadawo gefan kan Aimanah yasa hannunta cikin nasa "I love you Aimanah" murmushi tayi ta kauda kanta Dr na mata dariya "Ranka yadaɗe zamu kwarfe mata jini yakamata ka bamu waje" "Baki da damuwa dani Dr kiyi komai ina nan yau nan zan kwana" Dr dariya tayi tana canza safar hannunta "Wayyo" Aimanah tafaɗa sanda taji hannun Dr a jikinta "Aimanah mai nake ji kinji wani babyn fa" Dr Rubina ta faɗa tana ciro hannunta daga jikin Aimanah "Wani babyn kuma?" Aimanah da Musty suka faɗa a tare, kai dr ta ɗaga tareda kokarin yiwa Aimanah scaning hoton baby ya bayyana, Musty Lumshe ido yayi yana jero hamdala ga ubangijin da yayi masa wannan baiwar yara uku rigis lokaci ɗaya kai masha Allah, Aimanah wani sabon ciwon taji yana taso mata, tafara cize baki tana mimmikewa "Wasa farin girki" Dr Rubina tafaɗa tana kallon Musty "Dr yanzu wani leboor ɗin kuma zata sake?" "Da a lama" Awanni biyu suka shuɗe ba alamar fitowar baby har an fara kokarin yiwa Aimanah cs sai kuka sukaji Aimanah ta sauke numfashi tana kallon babyn, "Maca ce wannan" Dr Rubina ta faɗa tana jijjiga babyn ganin kukanta baya fita sosai kamar na sauran yaran "Nurse Fatima kai wannan babyn nursery wajan su Dr Auwal emargency bata da cikakiyar lafiya da alama tasha ruwan mahaifa, naɗe yarinyar A tawul nurse Fatima tayi ta fita da sauri ita da Ammi suka nufi ɓangaran yara na hospital ɗin, nan da nan Aimanah tai wanka ta shirya sai sannan Mah tazo hospital ɗin shima Ammi ce ta mata waya anyi haihuwa ta kawo ma mai jego abinci da tea, ɗakin na musamman aka kai Aimanah da babyn ta guda biyu ɗayar na sashin yara ana bata kulawa, Musty har sannan bai kalli yaran ba yana kusa da Aimanah yana dai kallo ana ta ɗaukan babyn wannan yaba wannan dan tuni yan uwa sun cika hospital ɗin kai baza kace dare bane musamman daya kasance haske gashin tar wai ko alluranka ce ta faɗi zata iya ganinta kaɗau kayar ka "Yayanmu babyn nan da kai yake kama" Ma'aruf yafaɗa sanda ya ɗau babyn a hannusa duka biyun "Ya Ahmad zokamin hoto da babyn nan a tura a group kowa yaga yau na girma" "So kake ka tashi hankalin Anty Hasana da daran nan tasa dr neman jirgi" Ammi tafaɗa tana dariya, Mah dai na gefe tana murmushi bata ce komai ba "Mustapha yaɗau yaran nan kuwa?" Mah ta tambaya tana kallon Mustaphan "Mah basai na ɗauke su ba tunda ga ku ai shikenan" "Mu daban kai daban, maza ɗauke su kamasu huɗuba ka masu kuma addu'a" kallon Aimanah yayi "Da alama dai ranka yadaɗe fushi kake da babys ɗin nan sun wahalar da madam" Dr Rubina ta faɗa tana kallon Mustaphan, dariya yayi "Aimahh wanne suna za'a saka masu?" "Daddy da Abba" yana kokarin karɓar yaran Alhaji Kamal da prop Farouk suka shigo ɗakin kana kallon fuskar su zaka hango zallar farin ciki, Musty fasa karɓar yaran yayi ya koma inda yake ya zauna Alhaji kamal ya karaso gaban gadon da Aimanah ke kwance yana mata sannu, yayin da Prop ya wuce ya karɓi yaran, fuskarsa da murmushi yake faɗin "Masha Allah bakin duniya, Sauda kalli yaran nan kamar Mustapha randa aka haifosa" dariya akayi gaba ɗaya, Alhaji kamal ya amshi guda ɗaya yana masa kiran sallah a kunne, Alhaji Farouk ma hakan yayi kamar yanda sunna take "Prop sai kayiwa kanku takwara ai" "To nidai na hannuna nasa masa Umar faroup" Prop ya ce "Au haka ne bari wannan to na masa huɗu ba da Muhammad Kamal" dariya aka kuma yi Dr Rubina dake haɗa allura zatayiwa Aimanah tana kallon Family ɗin tana yaba haɗin kansu. "Baby wai wannan allurar ni za'ayiwa?" Aimanah ta tambayi musty rai ɓace kamar zata yi kuka "bake zata yiwa ni za'ama madadinki" "A'a kadai faɗawa madam gaskiyya ita zanwa duk kun hanata barci gara tayi barci ta huta gajiyar nan" "Babban mutum ajjeni gida" Ammi tafaɗa tana mikewa tsaye, da sauri Mah ta tashi "Mai kike nufi wai na zauna anan Allah ya sauwaka" "Ai kuwa zama ya kama ki yaya tunda Momy na wajan Babyn can, ke ki zauna tareda Aimanah ni kuma naje gida na kwanta na huta tun rana fa muna nan" "To daman tunda kikayi jikoki ai tafiya ba taki bace na rantse maki bazan zauna ba kinga ma tafiya ta" Mah ta fice daga ɗakin "Ammi ni na zauna mana sai kije ke ki huta" "Tunda mahaukata ne mu ba, ga Aimanah batada gata ai sai mu barka da ita, tashi ma kabar asibitin nan mara kunya" "Ammi ki barsa mana basai ku zauna tare ba" "Na shuga uku ni saude, yau ga ranar Anty Hasana data nan data fige ku tas, to bazan barsa ya zauna ɗin ba tashi kaban waje" ba yanda Musty yaso haka yasa kai yabar ɗakin yana waiwayan Aimanh, itama idanunta na kansa🤣 Washe gari sassafe saiga Anty Hasana kamar daman a kasar ta kwana, agaba tasa jariran tanata kallo da yabawa, har inda ɗayar babyn take sai da taje ta ganta, tana zuwa hospital ɗin Ammi ta koma gidanta, kulawa ta musamman Ake bawa Aimanah ɗakin Shaheed daya tafi malesia karatu nan aka gyarawa Aimanah ita da babys ɗinta nan zasuyi zaman jego, kwanan Aimanah biyu a hospital aka sallame su har babyn data ji sauki ta murmure sai dai bata kai mazan girma ba, kulawa ta musamman Aimanah ke bawa babyn da aka sanyawa Saudat sunan Ammi kenan, haka kurum duk cikin yaran tafi jin yarinyar a ranta ganin itace mai lalura ga karamin jiki, mazan akwai cikakkiyar lafiya da kuzari karma Faruok yaji labari, kwanan Aimanah huɗu da haihuwa saiga Abbas da Rumana sunzo hannu biyu Mustaphaa ya karɓi Abbas sun jima suna hira nan falon Ammi sai da Abbas yata shi tafiya ya ce "Aimanah ga yar zaman wanka nan na kawo maki" yafaɗi haka yana kallon Rumana "Kai Hayatie nice yar zaman wankan fisabililahi" "Indai ba zaman wanka zakiyi ba sati nawa kika ce zakiyi ko inaga tare zakuyi jegon da Yaya Aimanah" dariya akayi gaba ɗaya Abbas da Musty suka fita, siyaya sosai Rumana tayiwa babys ɗin nan kaya masu kyau da tsada harda atamfofi guda uku wai inji Abbas, Sosai Anty Hasana ta tsaya a kai da fata ganin Aimanah tayi jego mai kyau abinci mai kyau da inganci take ci ko kusa bata wasa da cikinta dan sosai yaran ke yawan shan nono har saida Mustapha yai magana ko za'a haɗa masu da madara wai karsu ramar masa da mata, Anty Hasana ta ce la baza'ai haka ba, Sosai Mustapha ke kulawa da Aimanah ba ruwansa da yawan matan dake cika gidan kullum ko yaushe yana tareda Aimanah abokan wasa nata tsokanarsa, kwana biyar da haihuwa saiga manyan raguna guda uku daga Alhaji Farouk mai nera, kamar haɗin baki jimawa kaɗan saiga wasu ukun daga Abbah Alhaji Kamal, a ranar Sumayya tadawo daga legos tazo taga yara tanata yabawa da addu'ar Allah ya raya, Murjana ma tuni sunzo itada mijinta sun kawowa babys riguna guda goma sha biyu ta tafi tana faɗin sai ranar suna zata dawo, Surayya kullum sai anyi vidio call da ita taga babys wani bin har kuka take tana rokon Mas'ud daya barta tazo amma ya kafe ba inda zata tafi ta barsa a wata kasa, kayan fitar suna set sha biyu Mustapha yayiwa Aimanah, Sumayya kuma guda shida, tun saura kwana biyu suna aka fara soye soyan kayan snack su Anty Ruma da Rumana da Anty Ummi data zo daga london sune kan gaba wajan komai, Ranar suna mun sha shagali nan compound na gidan Ammi mukayi komai Anty Huda taso ɗakko mai dj Musty yamata jan ido kan baza'a masa kiɗa ranar sunan yaran saba, ranar suna kuwa sai ga masu kiɗan kwarya na gidan saraikai Anty Hasana ta ɗakko su ba yanda Musty ya iya dole yanaji yana gani aka cashe da kiɗan kwarya na gargajiya, sosai aka raba abubuwa babbar jaka ce mai ɗauke da hotunan yaran jota biro sai kayan snack da lemu da ruwa har da naman suna sune acikin ko wanne jaka, sai bayan insha aka tashi daga kiɗan yayinda su Rumana da Anty Huda suka sha rawa kamar ba gobe, tsab su Anty Ummi suka gyara gidan a washe garin suna, da ɗaya da ɗaya kowa yabar gidan daga Aimanah sai Ammi sai ko Anty Hasana da tace bata barin gidan sai nayi arba'in, Musty ma tuni shida Sumayya sun koma legos sai faman uban kiran waya da muke sha da vidio call ko yace na masa vidion yaran ya gansu haka zanyi na tura masa, Rumana tasawa Yaran Aslam Tasnim da islam Umar farouk shi u Ake kira da Aslam, Muhammad Kamal kuma Tasnim, Saudat ake kiranta da Islam, Aimanah jego suke na gata ga sabaya da Anty Hasana ta haɗa mata take dama mata kunun kullum tasa mata zuma da madara ta sha, kafin wani lokaci sunyi kuɓul ɓull ita da yaran har Islam ma ta murmure duk da bata kai su Aslam girma ba, Musty satinsa huɗu rabonsa da kano, yau suna waya Aimanah ke masa korafin rashin zuwan sa "Reina bafa wani abu ya hanani zuwa ba ayyuka suka tusoni a gaba ga transfer danake so nadawo kano cikin yan uwa na na haɗe ku waje ɗaya ku zauna keda Sumayya nan gidan yamana kaɗan innace zan haɗe ku" "Ni bazan yadda da wani uzurin ka ba kawai dai dan bani da abin baka ne shiyasa". "Bakiji haka a baki na Aimah" "Hakane mana rashin zuwanka ganin mu ya bayyana gaskiyya" bata jira mai zaice ba ta katse kiran ta saka number sa a black list a whatsapp ma tayi bloking ɗinsa, Murmushi yayi sanda yaga aikin datayi a fili ya furta "Aimah rigima" ba shiri washe gari asabar yatawo kano da yamma, Aimanah sai ganinsa kawai tayi, sosai yayi farin ciki da ganinta musamman ganin yanda tayi kiba ta kara haske kai baza kace jego take ba, duk yanda yaso ya keɓe da Aimanh Anty Hasana bata basa dama ba, sarai ta lura da zulamarsa akan Aimanah, yau da sassafe aka kira su Ammi Ana ba lafiya tana Anty Hasana da Ammi suka tafi hankali tashe, suna tafiya kamar Musty yasani ya shigo gidan yaji shuru baiga kuma gilmawar Anty Hasana ba yasan daman Ammi ba mazauniyar gida bace tunda tana fita aiki musamman daya kasance yau ɗin monday, Aimanah na rike da Islam tana bata mama Musty ya ɗan lego ɗakin ganin Aimanah ita kaɗai yabasa kwarin gwiwar shigowa ɗakin zama yayi kusa da ita ta kauda kai gefe "Aimah wai mai yasa kike da rigima ne kince naki zuwa na ganku kuma nazo ɗin ma baza a sakar min fuska ba" batace komai ba hannu yasa ya gyarawa Islam nonon da take tsotsa "Ni ka daina taɓa ni" Murmushi yayi yana kallonta kallon dayasan bata iya jure masa, ai kuwa tayi kasa da kai tana murmushi, "Ko kefa reina har kinsa raina yayi fari" saka Islam tayi a kafaɗa tayi gyatsa kana ta kwantar da ita cikin net ɗinta ta dawo nesa da shi kaɗan ta zauna "Bazan koma legos ba zan zauna nan kano na koma aiki na, Anty Sumy ta zauna acan" wani kallo yamata kallon baki isa ba kafin ya ce "Daman ke zaki zaɓa ma kanki inda zaki zauna" "Daman ai kasan abinda ya kaini legos kuma gasu nan sun fito Allah ya yaye min" baice komai ba sai matsowa da yayi kusada ita da sauri ta mike zata bar wajan ya roko hannunta suka faɗa saman gado, shi yana kasa yayinda ita kuma ta kwanta saman kirjinsa, hannu biyu yasa ya zagayeta ya haɗa ta sosai a jikinsa yana kallon fuskarta, kautar da kanta tayi gefe tana haɗe rai "Beb kalle ni, kisa idonki a idona nace" yafaɗa da muryar bata umarni "ke mao yasa kika fiye rigima ne, yanzu fa ba da bane kalli bebys ɗinki kin girma" "Ni ban girma ba Allah karka sake maidani tsohuwa" "Ai nima ba cewa nayi kin tsufa ba girma nace, girma daban tsufa daban" ta buɗe baki zatai magana ya haɗe bakinsa da nata ahankali yana tsotsar harshanta duk yanda taso ta kwace kanta ta kasa, gaba ɗaya yagama birkita mata lissafi, a wannan yanayin Anty Hasana tazo ta riske su, da sauri tayi baya ta koma ta maida kofa ta rufe su basu ma san ta shigo ba, jikin kofar ta tsaya tana maida numfashi haɗe da dafe kirji "Na shiga uku ni hasana ashe abinda zan gani kenan shi yasa Ana ta ce natawo gida na kula da mai jego" kofar ta soma bugawa da karfi, jiki sanyaye Musty ya janye Aimanah daga jikinsa yana gyara rigar Shaddar sa data tattare waje ɗaya "Wa ye?" yatambayya muyarsa a shake "Uwarka ce Mustapha nace uwarka ce, uban me kake a ɗakin mai jego?" zaro idanu Musty yayi jin muryar Anty Hasana yai saurin mikewa ya fito daga ɗakin kafin ta tara masa mutane kowa yaji abinda yayi, simi simi ya fito ta gabanta yabar falon bai ko kalli inda take ba, sai da ya shiga gidansa sannan yafarawa kansa dariya Sanda Aimanah taji shigowar Antyn gyara kwanciyarta tayi tai lamo kamar mai barci "Kyayi likimo mana Aimanah yar daɗi miji maza biye masa ya kuma ɗirka maki wani cikin kiyi kazamin jego ga ciki ga goyo" Anty nata mita ita kaɗai Aimanah batace kanzil ba tun tana barcin karya harna gasken yayi gaba da ita...✍🏻 [2/13, 4:45 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi na Ashirin da tara* "Wai Mustapha ya koma ne? tunda nadawo daga gidan Ana ban gansa ba" Ammi ta tambayi Anty Hasana, taɓe baki Anty Hasana tayi tana kyauda kai gefe "Ni nasan masa ne, Allah ne fa yai mana taimako da tuni kila Aimanah ta kuma ɗaukar wani cikin, nan fa nazo na tarar da shi ya tisa yar mutane a ɗaki yana latsata" Ammi dariya tayi kawai batace komai ba "Allah yaya saudai kisa yarinyat nan ta yi planing kafin ta koma dan da alama mahaifarta mai saurin ɗaukar ciki ce indai kina lisaafe da watan auran su watan Aimanah tara da kwana goma sha biyu ta haihu" "Yau nake ganin rayuwa au har kwanaki kika arga masu bayan watanni" "To yaya abinne ai daga aure sai haihuwa" "Allah ya kyauta amma Aimanah bazatai planing ba, dama can family ɗinmu bamasu yawan haihuwa bane azo kuma ayi wani planing daga baya azo ana nadama inaga fa duk cikinmu Yaya Aiahatu ce kaɗai ta haifi shida daga mai biyu sai mai ɗaya saini da yaya Mukhtar da muke da uku," "Kuma hakane yaya, Amma dai inzata tafi karta tafi ita kaɗai nida cewa nayi ko Gwaggo fulani za'ayiwa magana tazo su tafi tare kinga ta tayata kula da su Taanim" "Kuma fa hakan za'ayi bari Ana ta warware sai asa driver ya ɗakko ta daga ɗanbattan" Mustapha bai samu an maida sa kano da aiki ba, Abuja aka tura sa haɗe da garmin girma da lambar girmamawa, anan legus yabar Sumayya ya sauka Abuja nan ma dai gida aka basa karamin gidan da bazai ɗauki mata biyu ba inma an zauna zai zama a takure, hakan yasa ya fitar da kuɗi yasai dankareran gida babba plate hause ne ginin tsakiya Babban falo mai ɗauke da manyan ɗakuna kowanne da banɗakinsa a ciki ga kicin nan cikin falon da kuma wani babba a compount na gidan, shiya saka komai na gidan daya kamada da kayan gado manyan kujeru labilaye kayan kicin komai ya zuba iya yanda zai iya kicin komai yaji babu ce kawai babu duk wata na'ura akwai ta a kicin ɗin nan nan cikin falon da babban dake farfajiyar gidan, gidane da ya kawatu da bishiyoyi na yan gayu da furanni ta ko'ina, mai gadi yasa sai mai kula da fulawoyin gidan, sai da yagama komai sannan ya sanarwa dasu Ammi sukazo itada Mah da Anty Hasana da momy harda yayun Mustapha guda biyu mata da Ahmad da Murjana wacce keta yaba gidan tana hotuna tana turawa Sumayya dake legos, ga Daddy da Abba Sun yaba gida sosai sun kuma sanya albarka, Abinci mai kyau Mustapha yasa aka kawo masu da lemu da ruwa nan suka yini sai dare suka bi jirgin karfe tara na dare suka koma kano kowa na santi da yaba gidan Daddy har yayi shirin kwanciya yana kokarin kashe wayarsa kiran Mustapha ya shigo, ban gajiya ya masa har zai katse kiran Daddy ya kira sunan sa "Mustapha" "Na'am Daddy" "Gida yayi kyau sosai Allah yasa rai akayiwa, sannan Sumayya itace babba ita yakamata ta fara zaɓar ɗakin da yayi mata kafin Aimanah" "Insha Allah Daddy za'ayi yanda kace" "Masha Allah ubangiji yakara arziki mai albarka akuma ci gaba da rike amana harkar banki wuya gareta misamman kana ganin gilamawar kuɗi, ka tsarkake zuciyarka kagadai yanda gaskiyya ke kai ka gaba, rike gaskiyya da amana shike kai mutum ga matakin nasara, aci gaba da riko da gaskiyya a kuma kau da kai daga haram komai kankantar ta" "Insha Allah Daddy" "Yawwa Allah yamaku albarka ya kara haɗa mana kanku aci gaba da zumunchi koda bama raye" "Amin Daddy Allah yakara lafiya da nisan kwana mai albarka" "Amin Muhammad Mustapha" sallama sukayi Musty yaja gwauran numfashi yana tina yanda zasu kwaso ta da Aimanah idan yafara bari Sumayya ta rigata zaɓi, saboda rigimarta ya hana Sumayya ta biyo sa nan Abuja yace tabari yazo tukunna, yanzu kuma ga abinda Daddy yace Aimanah sun zubar da wanka, tuni Anty Hasana ta koma Qatar bayan ta gama tsuma Aimanah da ingantattun maganin mata wanda Antyn ta haɗa mata da kanta, sai wanda kawarta yar sokoto ta aiko abawa Aimanan, ziyara sukayi sosai itada yara da Gwaggo fulani mace mai kirki wacce batada son jiki ga tsabta da fara'a, kwanan su hamsin da biyu Musty yazo kano kwanan sa ɗaya sai ga Sumayya washe gari kuma ya haɗa su suka koma Abuja gaba ɗaya, Aimanah bin babban falon daya kawatu da manyan kujeru tayi da kallo tana kallon yanda aka kawata falon da kujeru, tsaye tayi tana bin ko ina da kallo tsaɓanin Sumayya data yiwa kanta mazauni a ɗaya daga cikin kujerun da ke falon, "Aimah kinyi tsaye baki zauna ba, Gwaggo ga waje zauna" "Kanuna min ɗakina zan shiga" kallon Sumayya yayi kana ya ce "Ku biyo ni" bayansa suka bi suka zagaya ko wanne ɗaki suka gani Aimanah ta fara magantuwa "Gida yayi kyau sosai Baby" Musty Sumayya ya zubawa idanu yana kallon yanda tayi kasa da kanta "Sumy wanne bedroom kika zaɓa?" da sauri Aimanah ta ɗago ta kallesa cikeda mamakin maganar sa "Duk wanda kace na shiga" murmushin gefan baki yayi yana kallon Aimanah, "Ga ɗakin ki can" yanuna mata wanda ke bangon yamma, bata ce komai ba ta yi baya ta shiga, "Nifa" Aimanah ta faɗa tana turo baki gaba "Ga wanda nai maki sha'awa can na kusa da na yara," batace masa komai ba ta shige ɗakin, ɗakun nan gaba ɗaya iri ɗaya ne ba wani abu daya banbanta sai ko kala na labulaye, rayuwa ta ba ruwan kowa da kowa ake tsakanin Aimanah da Sumayya, sumayya daman ma'abociyar son zaman ɗaki ce, girki kowa nasa yake sai ranar girkin ka kabawa mijinka, Aimanah tuni ta koma makaranta zatai Masters dgreee, Sumayya ma gurbin karatu Ya sama mata ta fara karatu sosai ta maida hankali ga karatunta batai sake ba kamar yanda tayi a baya, Mustapha yasami nutsuwa da kwanciyar hankali, yai kiba sosai kuɗi sun zauna ga aikinsa da yakeyi da albashi mai tsoka ga kasuwanci dayake yi shiyasa tako ina kuɗi ke shigo masa, Salman ɗan gwaggo fulani ya ɗakko daga ɗan batta yasama masa makarantar gaba da scoundry yafara zuwa yana karantar business, Mustapha mutum mai taimakon na kasa da shi, ya rungumi yan uwan Anan na Danbatta wanda basuda hali yana taimaka masu sosai, Yaran Aimanah kyawawa masu matukar kama da mahaifinsu karma mazan suji labari, sun girma sosai dan yanzu shekarunsu uku sun taso cikin gata da kulawar iyaye da gwaggo fulani dake ɗawainiya dasu, soyayya sai abinda yayi gaba tsakanin Mustapha da Aimanah, sosai yake kamanta adalci a tsakanin matansa Aimanah taci gaba da karatunta gefe kuma tana aiki da ɗaya daga cikin gidajan redion dake garin Abuja, itama tana taɓa kasiwanci na online tana ordar perfume da abays da takalma daga waje har atamfofi kusan ba abinda bata kawowa sai dai in bakace kana soba, Mah itada Daddy tuni suna kasar saudiyya shugaban kasa ya yiwa prof ambasada a kasar saudiyya Mah da Ma'aruf da Dadyy na can, gaba ɗaya yayun Aimanah ba wanda yake kasar kowa ya kama gabansa wasu na karatu yayinda wasu ke aiki a kasar da suke Sumayya yau baki tayi kawanta ne wanda suke karatu tare suka kawo mata ziyara suna zaune nan falo suna hira, Aimanah tadawo daga wajan aikinta yau bataje makaranta ba, gwaggo fulani da suke ɗakinsu itada yara suka fito tun sanda sukaji tsayawar motar ta, Salman ɗan gwaggo fulani ya shigo falon da sallama ya mikawa Aimanah car key ɗinta yana faɗin "Hajiya ga keys ɗin nan" "Yanzu dai bazaka daina kirana da Hajiya ba, nace in bazaka faɗi suna na ba kace min Anty mana" "Da dai yafi sauki kam" gwaggo fulani ta faɗa tana dariya "Yawwa salman bari na ɗakko maka kuɗi kasiyo mana hanta yau miyar alaiyahu nakeson yi a gidan nan naga kuma bama da hanta" Aimah tafaɗi haka tana tafiya zuwa ɗakin Al'Mustapha dake can karshan falo cikin wani lungu, gaba ɗaya kawayan Sumayya suka bi Aimanah da kallo wacce ita sam bata lura da suba, mintina kaɗan da dawo hannunta rike da kuɗi ta mikawa Salman, ya juya ya fita "Amma" Islam ta faɗa tana shigewa jikin Aimanah, ɗaga ta tayi sama tana mata wasa "Maman Hanif ta shigo ɗazu bakya nan" "Allah sarki bari na gama aiki zan dai shiga mu gaisa" Aimanah sai sannan taga bakin Sumayya ta karasa wajansu fuska a sake tana gaida su, suma faram faram suka amsawa Aimanah gaisuwarta taja yaran suka shiga bedroom ɗinta, Gwaggo Fulani ta koma ɗakinsu, Feenah ta kalli Sumayya ta buɗi baki zatai magana sai Leena ta ce "A'A kar ce komai mu shiga daga ciki" Feena hannun Sumayya taja suka shiga Bedroom ɗinta suka kullo harda saka key, zama sukayi gefan gado fina ta rike baki tana kallon Sumayya da mamaki "Wai yanzu Sumy wannan ce kishiyar taki daman?" "Ita ce" Sumayya ta faɗa a san yaye "Cab tabbas zaki ga takaici jibi yarinya sai iyayi kalli uban kuɗin da ta fito dasu daga ɗakin mijinta" "Mijinta kuma" Sumy ta kuma faɗa cikin sanyinta "To mijinta mana Sumayya ke kina zaune anan bazar kin saki jiki kina zaune da kishiya lafiya waya gaya maki ana zama da kishiya nifa nan da kika ganni sanda zan auri Alhaji na shiga malamai nayi na rabasa da matarsa da yayansa ya kaɗa ta can aka koma gida akaci gaba da cin tuwon dawa, na kama abina ram na rike yanzu in gaya maki daga ni sai ɗana muke abinda ranmu yake so mota sai wacce naso nake hawa, yanzu ki duba misali ace yau Mustapha ya mutu mai zaki samu a dukiyar sa sai dai fa aɗan tsakurar maki ɗan kaɗan, kizo muje inda za'a maidaki tauraruwa a idanun mijinki ya zama sai abinda kika ce shi za'ayi a gidan nan" "Bazan bi malamai ba, inkai zunubin ina" raɗa Lima tayi mata a kunne komai suka cewa Sumayya oho tadaiyi murmushi tai shuru tsawon lokaci kana ta ce "Ina son Musty tabbas nima zan so na haihu da shi zanyi abinda kuka ce yau she zamuje wajan malam ɗin?" "Basai munje dake ba can enugu ne wajan da nisa sosai indai zamuje kwana biyu muke yi, Mustapha zai barki kiyi tafiyar kwana?" "Zai bari mana, zan masa karya zani Kaduna gidan yayar babanmu nasan zai amince, ban taɓa ce masa zani wani waje ba ya hanani" "Yawwa yar gari toki tanadi kuɗi, Malam yana aiki kamar yankan wuka amma fa sai yaji dumus" Lina tafaɗa tana dariya "Banda matsala da kuɗi Mustapha nasamin kuɗi a acount ɗina duk wata bana amfani dasu tarawa kawai nake yanzu zasumin rana" nana suka rabu akan jibi zasu tafi enugu, koda Al'Mustapha yadawo ta gaya masa baiyi musu ba sai fatan sauka lafiya da yayi mata, sanda yace zai sai mata ticket anan ne tace bata son zuwa a jirgi mota zata bi, washe gari ta kira yar uwar babansu tafala mata tafiya zatayi ne bikin kawarta a enugu tasan in Mustapha yasan ga inda zata bazai bari ba tace masa nan zata zo, koda wata magana ta taso tace nan ta zo, jiki na rawa Matar ta amsa mata da to sukayi sallama Sumy ta tura mata dubu hamsin, randa sukai alkawari ranar suka tafi gaba ɗayansu ukun, Sumayyya tun tana tafiyar marmari harta fara galabaita sabida a enugun ma inda sukaje can wani kungurmin daji ne ba gida gaba ba gida baya, sai wata bukka saman tsauni haka su Sumayya suka hau tsaunin nan kafin suka rufe idanunsu lina na karanto masu wasu ɗalasimai wata guguwa ta ɗebe su, tai kamar zata buɗe idanunta taji anan faɗin "Karki soma kada ki sake ki buɗe mana idanunki anan, kina buɗe su sun zama banaki ba mallakin aljani tsunju" ai kara damke idanunta tayi har zuwa sanda taji guguwar ta tsaya taji wata murya mai kamar ana busa usur tana masu magana, Feena ta zungureta ta buɗe idanunta tai tozali da wani ramamman mutum dogo sosai ga rankwameman kai zaune saman fatar damisa" shekewa yayi da dariya yana kallon Sumayya "Yarinya burinki ya gama cika tunda kika zo nan ungo wannan" yafaɗa yana wullo mata wani kullin magani kulle cikin kyallan atamfa "Kimasa lemu ki tabbatar kinsa garin maganin nan to daga ranar sai abinda kika cewa mijinki duk abinda kika ce masa shi zaiyi zai manta da kowa da komai sai ke, hakama kishiyarki kowa nata zai manta da ita sannan zamu kafe ta a gidan komai zakiyi mata bazata iya barin gidan ba, gaba ɗaya dukiyar Mustapha ta zama taki sai abinda kika ga dama kika ce yayi shi zai yi" ranta ne yayi wasai taji gaba ɗaya kamar an yaye mata damuwar dake ranta, saidai jikinta ne yayi sanyi sanda taga Malam na saduwa da Lina ta bayanta anan ne hankalinta yata shi taga lina bata ko damu ba, agabanta ya kuma biyan bukatarsa da Feena, jikinta ne ya hau ɓari ganin malam na kallonta yana lashe baki "Ki nutsu bazanyi komai dake ba, bama bukatar irinki akwai sauranki sai nan gaba kema zakiyi abinda suka yi juye mana kuɗin jakarki" gaba ɗaya ta zazZzage masa kuɗin cikin jakar suka fita da baya da baya" "Lina mai naga kunayi da mutumin nan" "Wannan ba huruminki bane Sumayya kiyi kallo kawai kuma karki sake ki bawa kowa labarin abinda kika gani mun aikata da boka, wannan wata bukatar ce daban" hotal suka kama suka kwana...✍🏻 [2/13, 4:45 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi Na Talatin* Musty ke zagaya falon da gudu, yara da Aimanah na biye da shi suna dariya, kallo ɗaya zaka masu su matukar baka sha'awa Gwaggo Fulani na can karshan falon tana kallon ahalin dake cikin zallar nishaɗi, dukan su ba wanda ya iya kama Mustapha, zilliya yake masu kamar a filin kwallo, sai da yagaji dan kansa kana ya zube kan kujera Aimanah da yaran gaba ɗaya suka faɗa kansa suna faɗin "Yee mun kama Abbie mun kama abie" "Abie ni coculate zaka bani" Islam tafaɗa tana taɓe fuska kamar zatayi kuka "Abi mu kuma sweett muke so ko Aslam" Tasnim yafaɗa yana kalllon Aslam "Ba wanda zan bawa komai, sabida ba wanda ya iya kama ni" "Harni?" Aimanah ta faɗa tana taɓe fuska kamar wata karamar yarinya "Ni na'isa nace har ke, in ban baki sweet ba yaya zanyi da ita" yafaɗi haka yana shafa mararta, bakinsa kan kunnanta yake mata raɗa "reina inajin kishi fa, kizo muje ki bani ruwa" yafaɗa da wata irin murya da sauri ta ɗago kai ta kalli cikin idanunsa waɗanda suka tabbatar mata da abinda yafaɗa "Baby yara na nan fa?" "Ni ba ruwana da wasu yara" yafaɗa yana mikewa tsaye, kallonta yayi da runan nun idanunsa da suka fara canza launi, lumshe su yake a hankali yana buɗe su akanta, bayansa tabi ganin ya nufi ɗakinsa, yaran ma suka bi su, cak suka tsaya daga bakin kofar ɗakin Mustyn sanda Mustapha ya shiga "Amma, Abie ya shige bai bamu sweet ɗin ba, kuma kin hanamu shiga ɗakin sa" haɗa yaran tayi gaba ɗaya ta rungume su, dai dai nan Musty yafito da alawa da coculate yabawa kowa "Mungode Abie Allah yakara arziki" yaran suka haɗa baki suka faɗa gaba ɗaya "Amin maza ku wuce wajan Gwaggo ta ɓare maku sweet ɗin" da gudu mazan suka tafi, Islam ta makale jikin Aimanah tana yamutsa fuska "Ammi na wuce kije kinji bazan jima ba, Abie zan sa yayi barci ya huta yanzu zan zo wajanki" sakin Amman tata tayi ta tafi tana waigenta, Mustapha jawo Aimanah yayi suka faɗa ɗakin "Baby ka fiye rigima fisabilillahi da tsakar ranar nan" "Aimah bazaki gane ba" yafaɗa sanda suka faɗa gado, ta buɗi baki zatai magana ya haɗe bakinsa da nata yafara aika mata da zafafan sakonni masu wuyar karɓa🚶‍♀️ Sumayya basu shigo Abuja ba sai dare hakan yasa bata sami damar aiwatar da aikinta ba ta bari sai washe gari, ai kuwa washe gari sai dare kana Mustapha yadawo yariga da yafaɗa mata, tun yamma ta gama haɗa komai har lemun daya sha maganin da malam yabata ta jere komai bisa danning jiran dawowarsa kawai take, bai shigo gidanba sai bayan sallar insha yana shigowa ɗakin yara yafara shiga ya duba su kamar yanda ya saba, cake ya basu sunata murna sannan ya fito Aimanah na zaune a falon tana aiki a systam ɗinta, ya tsaya ɗan nesa da ita kaɗan "Sannu da dawowa Baby" "Sannu fa, ya kike ya gida da yara?" "Alhamdulillah gida lafiya" gaba yayi ya shiga ɗakinsa yai wanka ya shurya cikin jallabiya marun kana ya shiga ɗakin Sumayya dake kwance tana chat dasu lina, "Sannu da zuwa" "Yawwa" "Muje ko abinci na danning" jerawa sukai zuwa wajan damning area ɗin yana cin abincin a hankali yana satar kallon Aimanah dake can nesa da su ta dukufa tana danna systam da alama aiki take mai mihimmanci, murmushi Sumayya tayi sanda taga yakai cup ɗin lemu bakinsa, nan take yaji kansa ya wani sara masa, yai lu zai faɗi, Sumayya ta tallafo sa kamar wani mai jin barci ta gaban Aimanah suka zo suka wuce Sumayya na rike da shi, maimakon ta kaisa ɗakinsa saita shiga da shi ɗakinta ta kwantar da shi kan gadonta tana murmushi ganin yanda yai lamo kamar mara lafiya, Rawa tayi tai juyi ganin aikin ta yayi kamar yanda malam ya shaida mata, tana kallon yanda yake barci, malam ya tabbatar mata Wannan barcin idan yayi sa to yana farkawa zai manta da kowa, komai sai tace yayi sannan zaiyin, aiko hakance ta faru da asuba ya farka sai dai ji yayi jikinsa ya masa nauyi ya kasa ta shi, sai da Sumayya ta ce "Kaje kayi sallah" kana yasami kwarin gwiwar mikewa yai alwala yatafi masallaci, ko acan wani iri yarinka ji Allah Allah yake a idar da sallar ya dawo gida yaga Sumayya A ranar gwaggo fulani tasami labarin rasuwar babbar yarta tafiya ba shiri lokacin Mustapha na barci ɗakin Sumayya, ta kira wayarsa yafi a kirga bata shiga haka yasa tai Kncking na kofar Sumayya, lekowa Sumayya tayi tana kallon Aimanah a wulakance "Barka da safiya Sumy, dan Allah ki faɗawa Baby Anma Gwaggo rasuwa zata wuce kano" "Barci yake kuma yace kada a tashe sa" Sumayya nagama faɗar haka ta maida kofarta ta rufe tabar Aimanh baki buɗe, jiyowa tayi tana kallon gwaggo daketa rusar kuka Salman na lallashinta "Salman zaka iya tuki zuwa kano?" Aimanah tafaɗa a sanyaye "Bazan iya ba Anty bana cikin nutsuwa" "Shiryawa gwaggo kayanta, saina kaiku tasha" Aimanah da kanta takai su Tasha ta biya masu mota shata ta ɗaukar masu sukai ciniki ta biya kuɗin motar, gefe sukayi da Salman ta basa Atm card ɗinta "Salman karike wannan a hannunka dan Allah duk wata harka ta kuɗi inta taso ayi amfani da kuɗin ciki suna da yawa nasan zasu isa komai daga anyi bakwai ka dawo sabida makarantarka Gwaggo kuma ta zauna in mukazo kano nida Baby sai muje mu tawo da ita zuwa sannan ta gama amsar gaisuwa, motar har ɗanbatta zata kaiku na biyasa kuɗin sa" "To Anty Mun gode Allah yasaka da alkhairi" Salman yafaɗa yana share hawaye "Kadaina kuka Salman ka lallashi gwaggo Allah ya mata rahama ya raya abinda tabari" "Amin" yafaɗa tana kallonsa ya shiga motar suka tafi tana ɗagawa gwaggo hannu, sai da taga futarsu daga tashan kana ta shiga tata motar taja itama ta tafi gida, Aimanah canji tagani daga Mustapha daya zama ko kallon inda take bayayi bare kuma yaran, kwanaki huɗu kenan ko gaida sa tayi baya amsawa kullum yana ɗakin Sumayya daga yadawo a office ya shiga bazai sake futowa ba sai safiya, ko abinci Sumayya bata bari yaci nan falo sai dai a ɗakinta, tunda gwaggo ta tafi bataje aiki ba daman gwaggo take bari da yaran yanzu kuma bata nan, yau ta tarawa dawowar Mustapha haka yasa ta zauna nan falo tana jin tsayuwar motarsa ta fita compound ɗin da sauri dai dai zai shigo ita kuma zata fita, gefe tayi ganin yana kokarin ture ta, ta tsaya gefe "Yaya Mustapha yaya zanyi da yaran nan inason zuwa wajan aiki fa" "Kiyi duk yanda zakiyi da su, ke kada ma ki kara fita wannan aikin naki, and dan Allah ki rinka nesa dani banason ganinki" cak ta tsaya tana kallon Mustapha dake faɗar maganar nan cikeda mamaki, Sumayya dake tsaye jikin kofarta dariya ta saki tana tafa hannuwa kamar wata sabon kamu, hannun Mustapha taja suka faɗa ɗakinta, Aimanah bata gama shan mamaki ba sai washe gari da Sumayya ta risketa a ɗakinta lokacin ta idar da sallar asuba kenan tana azkhair na safiya, "Mustapha yace ki wanke masa motar sa, sannan ya ce nagaya maki duk wani aikin gidan nan daga yau ke zaki rinka yi kama da gyara compound wanke motocin gidan nan bawa fulawowi ruwa dan na sallami mai kula da fulawoyin jiya" Aimanah a fusace ta mike tana kallon Sumayya sama da kasa "Kije ki gaya masa bazanyi ba, ba aiki nazoyi gidan nan ba, ke Sumayya ki fita a idanuna miji ne kin janye sa nabar maki ki jiƙa abinki ki sha amma ki sani kinyi tsararo wallahi kisa na maki bauta a cikin gidan aure na" Aimanah na gama faɗar haka ta fice daga ɗakin zuwa kichin ta ɗorawa yara abin break, wayam taga store ɗin babu komai, afusace ta fito ta banka kofar ɗakin Sumayya ta shiga, Mustapha na zaune gefan gado yadafe kansa da'alama da abinda ke damunsa, "Malama ina kika kai mana kayan abincin cikin store" Aimanah tafaɗa tana kallon tsakiyar idanun Sumayya "Shi yace na kwashe su ana masa ɓarnar Abinci" "Mustapha kai kafaɗi haka?" Aimanah ta tambayesa tana kallon sa, kai kurum yaɗaga alamar e "Fine" Aimanah ta faɗa tana ficewa daga ɗakin, yaranta ta ɗiba suka fita babban store ta je tayo siyayya sosai ta jibge su a babban kicin ɗin dake comopound nan take komai nata daga ta gama tasa key ta rufe ta koma ɗakinta, Sumayya bayan Mustapha ya fita ɗaki ta koma tasa key ta kira lambar malam da fina ta bata bayan sun gaisa take masa bayani kan Aimanah "Ranka yadaɗe malam yarinyar nan fa sam bata tsorona in na bata umarni bata yi, ɗazu fa kawai dan nace ta wanke mana motocin gidan nan baka ga yanda tayo kaina ba kamar zata dake ni" "Sumayya yarinyar tanada hatsari banajin zan iya komai a kanta sabida a tsaye take kan ibada da azkhar amma zan duba inga ta inda zamu ɓullo mata" "Yawwa malam ka duba ɗin dan Allah nasan dai ai babu abinda ya gagare ka" shekewa da dariya malam kibauu yayi kana ya kashe wayar sa. Murjana kuka sosai take tana kallon Amarya dake zaune da wata yaloluwar doguwar rigar barci da alama bata jima da tashi a barci ba "Mama banajin daɗin ganinki da nake a wannan gidan da aka maida tsaɓon Allah ado a cikinsa, Mama dan Allah kizo muje ki bawa Abbanmu hakuri yamaidaki ɗakinki, inma bazaki koma gidan ba ki koma katsina gaban iyayanki please mama, abinda yakamata ace mu mukeyi kina mana faɗa shi kike yi mama" Mirja tafaɗa cikin matsanancin kuka "Murja ki fita sabagata kin riga kin girma kinyi hankalin kanki ki zaɓi rayuwar dazakiyi nima na zaɓi tawa, ca nake nan nazo maki da zaɓi na kika nuna ban isa ba kika zaɓi wanda ranki yake so, kije ki zauna da shi, yanda bana zuwa inda kike nima dan Allah ki nesanta kanki dani, basu Saudatu kika maida iyayanki ba to kije na bar masu ke" "Mama...Murja ki fita nace kafin na saɓa maki" murja mikewa tayi ta futa tana kuka, motar Alhaji Jamil dake jiranta a kofar gidan ta buɗe ta shiga ta zauna a mazauni gaba tana ci gaba da kukanta, Ahankali Alhaji Jamil ke tuki har cikin ransa yake jin kukan da Murja keyi hakan yasa ya faka motarsa gefan hanya ya kashe ta yai shuru yana sauraron shashshekar kukan Murja "Murjana dan Allah ki daina kukan nan, nasan dai akan mama taki amincewa ta koma gidan Abba ne, kiyi shuru kuka baya maganin damuwa kiyi addu'a itace maganin duk wata masifa" Kai kurum ta ɗaga alamar to kana ta ɗago fuskarta tana share hawayanta da hijab ɗinta "Haba ko kefa, jibi yanda kika ɓata min kyakkyawar fuskar nan taki" Murmushi Murja tayi tana daɗa jin son mijinta can kasan zuciyarta, Alhaji Jamil tukinsa yaci gaba jefi jefi yana kallon Murja, tausayi take basa sosai, ganin yanda batai dacan uwa ba, a zaman da yayi da ita ya fuskanci tanada saukin hali rashin dace da mahaifiyar kwarai da batayi ba shiya jefa ta ga rayuwar bariki wacce ta dalilinta har tayi rashin mahaifarta, yana matukar tausaya mata musamman ganin yanda take matukar kulawa da yaransa uku gaba ɗaya komai nasu itace tun sanda ya aureta kulawarsu gaba ɗaya ta dawo kanta musamman in suna kasar, daman Mamansu ba wani kulawa take da su ba aikin ta da kasuwancinta su kawai tasa a gaba nanny ke kula da su da ita suka saba sai bayan zuwan Murja suka san daɗin uwa. Abbas ya shafi cikin Rumana mai watanni biyar, yana murmushi "Kana son cikin nan dayawa Hayatie" "Sosai nake son sa, karo na farko ciki ya kai wata biyar a mahaifarki insha Allah wannan zai zo duniya" "Allah yasa Hayatie, ni duk bansa rai ba kawai ji nake a kowanne lokaci zamu iya rasa sa kamar yanda muka rasa guda uku a baya" "Ki daina faɗar haka dan Allah masoyiya insha Allah zamu ga ƴaƴanmu harma da jikoki" "Anya kuwa, kasan yanda nakeji kuwa ni kaɗai nasan azabar da nake sha gani nake kamar mutuwa zanyi hayatie" Rumana ta faɗa tana fashewa da kuka, gaba ɗaya hankalin Abbas yatashi ya rungumota jikinsa ahankali yana share mata hawaye "Ki daina ambaton mutuwar nan Rumy ki daina bana so, in kika ci gaba wata rana zakisa zuciyata ta buga na rigaki barin duniyar, zuciyata zullo take aduk sanda kika ambaci mutuwa, muna tare ni dake zamu rayu tare zamu mutu tare Insha Allah rana ɗaya lokaci ɗaya zamu mutu amma ba yanzu ba" yafaɗa yana sumbatar kumatunta. Sumayya malam waya yayi mata akan tazo ga aikinta ya gama ta karɓa, hakan yasa washe gari ta ɗauki hanyar enugu, a jirgi taje shiyasa bata wani ɓata lokaci ba tana zuwa tsaunin da malam yake tahau kamar yanda sukayi wancan zuwa wannan karan ma hakan tayi malam wata koshashshiyar mage ya wullo mata ta cafe "Kishiyarki nada hatsari sosai, indai wani abu zamiyi mata bazai taɓa kamata ba, sai dai na biyo mata ta bayan gidan, wannan magen da kike gani kisata a karkashin gadonki kar ki bata abinci ba ruwanki da ita, ga wannan" yasake wulla mata garin magani a cikin kwalba "Ki jika shi ki sha, sanda zaki sha ki ambaci sunan kishiyar taki zata rinka jin tsoronki kuma duk umarnin da kika bata zata bi, hhhhhhh gida ya zama naki yarinya sai dai mumada sharaɗi zaki daina sallar asuba da la'asar a maimakom sallah biyar uku zaki nayi kina jinmu" jikinta na rawa hannunta na kankame da magen da ke ɗan kuka kasa kasa ta ɗaga kanta dan bakinta yakasa furta komai sabida tsoro da firgi cin daina salloli biyu da aka sata, ta fita da baya baya Shatar mota ta ɗauka a tasha zuwa abuja sassafe ta isa gidan ta dake abuja, tayi nasarar tarar da Mustapha baya nan ya fita aiki, hakan yabata damar saka magen kasan gado ta kuma zuba ruwa a kwalba mai magani da malam yabata ta shanye...✍🏻 [2/13, 4:45 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi Na Talatin da ɗaya* Aimanah dake kwance a ɗaki gaba ɗaya taji jikinta kamar wacce ake ɗaurewa da igiya duka jikinta yayi sanyi kalau, lamo tayi tana kallon yaranta dake barcin safe, banko kofar da akayi da karfi ita ta farkar da Islam dake rigima daman barcin nata ba wani nisa yayi ba, Aimanah ta ɗaga kai ta kalli Sumayya dake girgiza tana wani fari da idanu "Ki fito ki gyaramin gida malama" Aimanah ta ɗago da niyya maida marta ni amma wani abu mai kyalli ya fito daga idanun Sumayya ya faɗa idanunta da sauri tayi kasa tareda runtse idanun nata, dariya Sumayya taci gababdayi tana kallon Aimanah data sun kuya tana murza idanunta, da sauri ta ɗago bayan taji idanun nata sun daina zafin amma kallon da Sumayya ta mata yasa gabanta ya faɗi ba musu tabi Sumayya zuwa compound ta soma aikin data saka ta, daga wannan ranar saiya zamana komai na gidan Aimanah keyi ta koma kamar mai aikin gidan, ko abinci ita keyi amma wanda Sumayya ke bata ko yaran baya isa, Aimana na cikin damuwa sosai nan da nan ta rame tai baki sau biyu tana kwada son futa ta gudu daga gidan sabida azabar da Sumayya ke gana mata amma getman ya hanata fita, Maman Hanif makociyar su Aimanah ce tasu tazo ɗaya sosai lokaci bayan lokaci suna zagaya juna su gaisa, Maman Hanif ganin kwana biyu Aimanah bata shigo mata ba hakan yasa yau ita ta shiga gidan, abinda ta gani ya ɗaga mata hankali ganin Aimanah kamar mata yarinyar gida tana rike da moper tana goge compound na gidan da sauri maman Hanif ta taɓa Aimanah, Aimanah ta juyo tana kallon ta, sharr sai hawaye daga idanun Aimanah, gefe Maman Hanif taja Aimanah suka zauna "Maman Hanif ina cikin masifa kalli yanda rayuwa ta juyamin baya, Mustapha yadaina kulani komai na gidan nan ya canza jibi yanda nadawo yar aiki a cikin gidan mijina nakasa taɓuka komai ko na ɗaga waya zan kira makusanta na saina kasa nayi yunkurin barin gidan nan na tafi namu gidan an hanani fita ina zan saka kaina ban saba da wahala bazan iya wannan bautar ba" Maman Hanif goge hawayan idanunta tayi ta ruko hannayan Aimanah "Aimanah kina addu'a kuwa kina azkhair yanda yakamata" "Inayi Maman Hanif ina komai har karatun kur'ani ina yi" "Aimanah na rantse da Allah asiri aka maku aka farraka tsakaninki da Mustapha, ki tsananta addu'a ki daina barcin dare kina ta shi cikin dare kina addu'a Allah zai fiddaki daga wannan jarabawar daya maki, sannan karki gayawa kowa wannan maganar ki rike sirrin cikin gidanki" "Maman Hanifa nabar maganar nan fa kika ce karna faɗawa kowa na zauna cikin uku ba da azabar aikin nan harta motocin gidan nan ni nake wankewa" "Aimanah kiyi hakuri" maman hanif ta faɗa bayan ta mike tun daga wannan ranar Maman Hanif ke kawowa Aimanah abinci a ɓoye wanda zai ishe su, Sumayya duniya ta mata yanda takeso sai facaka take da kuɗi tana abinda take so, tsadaddiyar motar Aimanah yanzu ta zama mallakinta da kanta tasa Al'Mustapha ya karɓar mata key ɗin daga hannun Aimanah yabata, a cikin wannan halin da suke Rumana ta haifi yaranta twince masu matukar kama da Abbas mace da namiji, Hajiyar Abbas jigawa ta wuce da yaran da mai jego acan zasuyi zaman wanka Abbas ma kwana huɗu da haihuwa yabi matarsa wai tare zasuyu zaman wankan, Hajiya Hafsatu mace mai kirki da son mutane ita tayi ta kula da Rumana Ammi da taje ma bata barinta tayi komao harta ɗora ruwa yiwa mai jego da jarirai wanka duk ita takeyi, Aimanah taji labarin haihuwar tayita ɗoki da zumuɗin zuwa suna amma Mustapha yasawa idanunsa toka yace ba inda zata, wannan duk huɗubar Sumayya ce, Aimanah tayi kuka ranar kamar ranta zai fita, ta duba duka account ɗinta gaba ɗaya bata da komai a ciki duka ta cinye su lokacin da Sumayya ta ɗebe kayan abincin gidan, sai da dare yayi kana ta kira lambar Yaya Mus'af bayan sun gaisa ta ce "Yaya dan Allah kuɗi nakeso" "Kina matar accounter kike neman kuɗi, ko bashin banki basai yabaki ba" Mus'af yafaɗa yana dariya "Yaya banaso yasani fa, shiyasa nabari sai yanzu na kiraka, wasu kaya zanyi ordar nake neman kari" "kamar nawa" "Ko ɗari da hamsin nasamu" "Bama masu yawa kike bukata ba, ba damuwa zansa maki yanzu" "Nagode yaya" Aimanah tafaɗa tana share hawayan idanunta "Ba godiya a tsakanimu ina mutanan" "Sunyi barci tafaɗa tana kallon yaran dake barci" basu jima da sallama ba taji alart tana dubawa taga dubu ɗari biyu, murmushi tayi nan take ta yiwa Rumana transfer na dubu ɗari tareda mata messages _kiyi hakuri Rumana bazan sami damar zuwa suna ba anma zan zo daga baya naga babys ga kuɗi nan ba yawa asaiwa yarana riga_ Rumana murmushi tayi bayan ta gama karanta messages ɗin Hankali tashe Mustapha ke kallon Sumayya "Ina kika saka min jakar da jiya na shigo da ita," "Jaka kuma na rantse ni banga ka shigo da jaka ba gidan nan" Sumayya tafaɗa tana zare idanu, a haukace Mustapha ke bincikar ɗakin ko ina lekawa take ko zau gano jakar, rasa wannan jakar kamar rasa aikin sa ne, ga zargin cin amana da za'a masa kilama takaisa ga birsin hakan ya kuma tasar hankalinsa "Sumayya ki fito min da jakata nan fa na ajjeta" "Na rantse ban ɗaukar maka jaka ba, in baka yarda ba muje ɗakina ka bincika daga nan sai a duba na Aimanah" sak yayi yana kallonta jin ta ambaci Aimanah sunan da a yanzu bayajin akwai wani suna daya tsana ko son ji bayayi sama da sunan, ɗakinta aka bincike tas babu jaka ba dalilinta, haka ta tisa Mustapha a gaba aka shiga ɗakin Aimanah, ita tsorama taji daga gansu sun ahigo mata bako sallama mikewa tayi tsaye tana kallonsu "Kin wani zuba mana idanu kamar na mujiya jaka ake nema a gidan nan ba'a ganta ba, shine nace a bincika ɗakin kowa dan a fitar da ɓarawo, nagodewa Allah an bincika ɗakina bata nan shuyasa na rako sa a bincika nan" "Ok bisimillah" Aimanah tafaɗa tana matsawa suka shiga ɗakin sosai, bin ciken farko saiga katuwar jakar mai shake da manyan kuɗaɗe a cikin wardrove ɗin Aimanah, wacce tayi tsuru tsuru tsoro duk yakamata ganin abinda bata zata ba "Ka gani ko kaga gaskiyya ta fito ko, shiyasa nace a bincika ko ina, oh ana zaune da katuwar ɓarauniya bamu sani ba," Mustapha baice komai ba ya rungumi jakar kuɗi zai fita da ita "Wai kana nufin baza kace komai ba, kana ganin wannan babban zunubin da ta aikata sata fa" "Maizan ce Sumy tunda sun fito ai shikenan" "Au haka zakace ai wallahi bazan zauna da ɓarauniya anan ba wataran ni ta sace ni yau yau ɗin nan zata bar wajan nan daga ita har ƴaƴanta amaidata can ɓangaran bayan nan ta karata acan" "Duk yanda kikai dai dai ne" Mustapha yafaɗi haka yasa kai yafita daga ɗakin, watsi Sumayya tafara yiwa Aimanah da kayan sawarta dana yara tana watso su waje "A fita afita a koma can aci gaba da sata" Aimanah na hawaye ta fara tsintar kayanta ta ɗago ta kalli Sumayya zuciyar Aimanah ta rauni kawai ta fashe da kuka, kafafun Sumayya ta rike "Sumy na roke ki da girman Allah da azabar da kike gana mana gara kisa Mustapha ya sakeni na koma gaban iyaye" Sumayya ta kece da mahaukaciyar dariya tana kallon Aimanah "Saurin me kike ai ana gab da yin hakan zan saka ya baki takarda mai ɗauke da saki uku ta yanda ke da zama da shi har abada amma sai bayan na gama shayar da ke zumar azaba a gidan nan" Sumayya na gama faɗar haka ta juya ta wuce ciki ta rufo kofa, Aimanah kayanta ta ɗiba zuwa bayan wajan yayi datti sosai sabida da Salman ɗan gwaggo ke zaune a wajan babban falo ne sai ɗaki ɗaya mai ɗauke da toleit a ciki, kayanta ta jera a wardrove ta zauna gefan karamin gadon taja tagumi tana hawaye Tasnim na goge mata, Islam da Aslam na kwance lamo a jikinta, Aimanah duk yanda taso ta gayawa wani halin datake ciki saita kasa kamar wacce aka rufewa baki, hakan yasa ta tsananta ibadarta barcin daranta ya koma rabi cikin dare take ta shi tayi sallah tai kuka ta roki ubangiji ya fitar dasu daga halin da suka shiga, ko kaɗan batajin haushin Mustapha sai ma tausayinsa datake ji daman can tasansa da rauni musamman wajan azkhair sau tari ko addu'ar kwanciya barci ita ke masa ta shafa masa a jikinsa bare kuma azkhair da ada intayi magana sai yace aikine ya masa yawa zai yi, tasani wasa da azkhair da karatun kur'ani da yake shiya jawo masu komai, sabida ta tabbata Sumayya asiri tayiwa Mustapha kamar yanda tayi a baya sanda zata aure sa, Sumayya shewa sukayi da kawayanta suka tafa "Gaskiyya lina ina godiya da kuka ɗorani a hanya kuga yanda nadawo wata big girl da na tsaya kaina zai kulle, ai ingaya maku a gidanna mulkina nake yanda naga dama komai na Muatapha yanzu yadawo nawa harta motar Aimanah yanzu ni nake hawa da kaina na koma wajan malam kibauu nasa ya hana waɗan can mutanan dawowa nace a janyw masu hankali daga nan bare su dawo suga abinda ke faruwa atafi a lalatamin aikina yanzu ba gashi ba inata shan sharafi na, boka ya tabbatar min da Aimanah bazata iya barin gidan nan ba inhar ma magen karkashin gado na kunce ba," tafawa suka daɗa yi tareda shewa, Aimanah komawa tayi ta jingina da bango tana hawaye "Mage mage a karkashin gado ya ilahi" komawa Aimanah tayi da baya daman Islam ke kukan tana jin yunwa ta zo ta roki Sumayya ta taimaka ta bata abinci ashe rabon zata jiyowa kanta ne, wayar maman hanif ta kira mintina kaɗan tsakani Hanifa babban ɗiyarta ta kawowa su Aslam abinci, Aimanah zuru tayi tana kallon yaran ganin yanda suke cin abincin hannu baka hannu kwarya, share hawayanta tayi tausayin yaran suka kamata tamike tana jin zuciyarta na mata wani irin zafi zagayan neman mafuta a rayuwarsu tafara yi, kakarin aman data jiyo daga bayanta yasa ta juyowa taga islam ce keta amai da sauri ta rungomo yarinyar jikinta tana mata sannu, wajan datai aman Aimanah ta gyara, kafin wani lokaci zazzaɓi mai zafi ya rufe islam sai surutai take, "Wayyo Ammi zan mutu afaɗawa abie banda lafiya a kaini asibiti wayyo Ammi cikina" islam ke faɗa da muryar yara "Yi shuru islam bazaki mutu ba, zakiji sauki Aslam ne ya mike da gudu ya fita ya zagayawa wajansu Sumayya bako sallama yafaɗa ɗakin kai tsaye wajan Abie ɗinsa yaje ya ruko hannunsa "Abie islam bata da lafiya zo kaje ka ganta" Mustapha saroro yayi da idanu yana kallon yaran yana son tina inda yasan sa "Kai maye baza shi ba, futa ka bamu waje ɗan iska mara tarbiyya" Sumayya ta faɗa a zafafe kamar tana magana da sa'anta, Aslam baya yayi ya fita daga sashin yana legen Mustapha wanda shima yaron yake kallo wanda yake hango fuskarsa a fuskar yaran Islam tasha wahala matuka maman Hanif ta kawo mata magani harta sami sauki, yau Murja garin abuja suka sauka dawowar su kenan daga dubai jirgi ya sauke su nan abuja, hakan yasa ta cewa Alhaji Jamil ya kama masu ɗaki a hotal su kwana zataje gidan yayarta su gaisa, texz ya ta shiga zuwa Yaya Mustaphan cikeda ɗokin ganin yayar tata da yayanta harma da yaya Aimah, hannu biyu Sumayya ta karɓeta suna hira kan mahaifiyarsu "Anty Sumy yanzu wai ba wanda mama take jin tsoro yamata magana ta daina harkar datakeyin nan" "Babu Murjana iyayanta ne to suma sun zuba mata idanu duk da na tabbata basu san mai take aikatawa ba, duk da daman can bata ɗauke su da mihimmanci ba, addu'a kawai zamuyi mata" kai kurum Murjana ta gyaɗa can ta ce "Yanaji gidan shuru ko Yaya Aimah bata dawo daga aiki ba" dariya Sumayya tayi ta ruko hannun Murjana suka fito can baya karshan gidan Sumayya ta tura kofa suka shiga Aimanah ce zaune saman carfet itada yaran data rungumo su duka a jikinta, Murjana kallon Aimana tayi ta juya ta kalli Sumayya dake ta murmushi "Murja yaushe kika zo?" Aimanah ta tambayeta a sanyaye "Yanzu" Murja tabata amsa tana bin ɗakin da kallon mamaki, ta juya ta kalli Sumayya da har sannan fuskarta ke shimfiɗe da murmushi "Anty Sumy ban gane bafa mai Aimanah take anan wajan da ya dace ace yan aikinku ke wajan" "Itama yanzu ai batada maraba da yar aikin" Sumayya ta faɗa tana jan hanun Murjana dake kallon Aimanah wacce ke goge hawaye suka fita "Sakar min hannu Sumy ki sake ni, mai abinda na gani yake nufi" "Kin rigada kinsan komai Murjana wani malami na samu mai zafi ina gaya maki hmmm ba'acewa komai, aiki yayimin yanda nakeso, kema in kinason kama mijinki kizo na rakaki kiga yanda ake aiki kamar yankan wuka" "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, la'ilaha illa anta subahanaka inni kuntu minal zalimin, maine haka wai Sumayya kinyi hauka ne, ina zaki kai wannan zunubin mai girma haka" "Istigifari ai bai bar komai ba murjana inaka aikata ba dai dai ba saika tuba ka koma ga Allah" "Sumayya banso ba banso kika komawa harkar asiri ba duk karyan banza ce da ɗaukarwa kai zunubi kisani Allah baya yafe laifin wani daka cuta, Anty Sumy kin cutar da masoya Allah bazai barki ba, kuma da ikon Allah saina tarwatsa komai" Murjana na gama faɗar haka tayi baya ta koma wajan Aimanah da har sannan ta sameta tana hawaye "Yaya Aimanh bar hawayan nan insha Allah komai zai wuce yanda na tarwatsa wancan asirin haka yanzuma insha Allah saina tarwatsa komai, nasanki ada kinada ibada kici gaba karki daina tabbas nasan ibadarki tasa kika tsaya iya wannan halin, kaico kaicon yaya Mustapha da bai ɗauki azkhair da mihimmanci ba shiyasa daga an masa abu yake saurin kama sa kici gaba da addu'a Yaya Aimaah, ko zaki bini mu gudu na maida ke kano" "Bazan iya nayita yunkurin yin haka amma sai naji na kasa barin gidan zan so ace zan iya fita daga gidan nan da tuni bana cikinsa" mikewa Murjana tayi tana gyara zaman jakarta dake saɓe a kafaɗarta "Gobe zan dawo Yaya Aimah da ikon Allah saina fiddaki daga wannan gidan" ɗagowar da Murjana tayi taga Sumayya na tsaye jikin kofa tana kallon su, sa kai Murjana tayi ta raɓa ta gefanta ta wuce tana gafda fita daga gidan taji Sumy ta kira sunanta ta juyo tana kallonta "Zaki fitar da ita ko? to gara ma kiyiwa gidan nan kallon karshe keda sake shigo sa har abada" juyawa Sumy tayi ta koma ciki, Murjana jikinta yayi sanyi tana mamakin Sumy, Sumy na komawa ɗakinta malam ta kira ta sanar mata yanda sukayi da Murjana sannan tace tana so yakara mata aiki sosai kan Mustapha taga yafara mata musu kwanan nan "Dole zai maki masu kishiyarki na tsaye kan addu'a bamuda wani abu da zaiyi tasiri a kanta, kici gaba da rikon magen nan ruhin haɗe take da ruhin Aimanah daga randa kika yi sake magen nan tabar cikin gidan daga ranar Aimanah bazata sake kwana a gidan nan ba, fitar Aimanah daga cikin wannan gida dai dai yake da tarwatsewar komai da kikayi, ga tukunya nan mun saka aljani dundurusu ya ajje maki a kofar ɗakinki ki fito ki ɗauka ki mata ma ajjiya mai kyau karta fashe inta fashe akwai matsala maganar kanwarki kuma yanzu zan mantar da ita komai" sallama sukayi da boka Sumayya ta fita ta ɗauki tukunyar a hankali tasa can wani ɗan lungu dake cikin ɗakinta ta adanata Kamar yanda malam yafaɗa hakance ta faru Murjana kafin ta karasa hotal ɗin da suka sauka ta manta da wata Aimanah bare kuma alkawarin komawa datayi mata Yau Aimanah ta tashi jikin Islam ba daɗi gaba ɗaya hankalinta ya tashi musamman ganin yanda take mimmikewa, kafin wani lokaci ta suma yafi sau biyu, a guje Aimanah tafita daga wajan nata tai sa'ar ganin Al'Mustapha tsaye jikin motarsa suna magana da Sumayya da alama fita zaiyi "Yaya dan Allah dan Allah akai Islam hospital wallahi batada lafiya sumanta uku a safiyar nan, dan Allah Sumayya ki taimakamin" Aimanah tafaɗa tana rike kafafun Sumayya, Sumayya kafa tasa ta take hannun Aimanah wanda har sai da hannun yayi kara, Aimanah tasaki azababban ihun dayasa Mustapha lumshe idanu ya kifa kansa saman motar sa haɗeda rike kirjinsa da hannu ɗaya "Muna fuka baza'akai tan ba ta mutu mana waye a ciki" Aimanah mikewa tayi daga tsugun nan datayi na rokon Sumayya, hannunta wani irin azabar zafi yake mata tana fitar da numfashi ta kalli Sumayya cikin kukan azaba "Allah yamaida maki mugun nufinki kanka, Sumayya insha Allah bazaki taɓa gamawa da duniya lafiya, bazan taɓa yafe maki wannan azabar da kike gana min ba, nasani bazan zafi da raɗaɗin haihuwa ba tunda baki taɓa yinta ba, shiyasa bazaki taɓa jin tausayin yara ba nabarki da Allah" "Ni kike zagi Aimanah ni zakiyiwa Allah ya isa," "Ya isa ya isa haka Sumayya akai Islam hospital" Mustapha yafaɗa cikin bada umarni ya shiga motarsa yaja a fusace ya fice daga gidan da mugun gudu "Bazan kaitan ba idan ta mutu ma nima nayi farin ciki" Sumayya tasa kai ta koma ciki, Aimanah ɗaki ta koma ta kira lambar maman Hanif tana kuka ta gaya mata halinda Islam ke ciki, maman Hanif Dr ɗin dake duba su ta kira a waya yazo suka shiga wajan su Aimanah tare....✍🏻 [2/13, 4:45 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi Na Talatin da biyu* Dr yakalli Aimanah cikeda damuwa yace "Garin yaya akayi sake haka har olsa maleria da typoid suka kama wannan yar karamar yarinyar da bata haura shekaru huɗu ba" Aimanah ta share hawayen takaici tama kasa cewa komai ido kawai ta zubawa Dr ɗin "Dr lalura ce kawai Allah ya saukar mata ayi duk abinda yadace yanzun" Maman Hanif tafaɗawa Dr ɗin, Drip dr yasawa Islam yace a kula sosai da hannun bari yaje ya ɗakko allurai da magunguna yadawo, Maman Hanif ta dafa kafaɗun Aimana da hawayan fuskarta suka ki tsayawa "Dan Allah kibar kuka Aimanah, komai na Allah yanada iyaka insha Allah komai zai wuce ku dawo normal rayuwarku mai daɗi irin tada koma fiyeda haka" Aimana fashewa tayi da matsanancin kuka tana kallon Maman Hanif "Nagama auran Mustapha addu'a nake yasakane ni na kama gabana maman Hanif aure ma gaba ɗaya bazan sake ba, aikina zanci gaba da yi na rungumi yarana shi kuma yaje su karata da Sumy ko kashe sa tayi ita ta jiyo" "Daina faɗar haka Aimanah ba rabuwa tsakaninki da Mustapha insha Allah" lamo Aimanah tayi ta zauna kamar wata karamar yarinya xuciyarta na mata wani irin zafi Ammi "Abba kuna waya da Mustapha kuwa?" Ammi dake haɗawa Abba cofee ta tambayesa idanunta nakan abinda take haɗawa "Muna waya ko yauma munyi ɗazu ina kasuwa ya kirani mun gaisa yace abubuwa ne suka masa yawa shiyasa bai shigo kano ba kwana biyu" kai Ammi ta gyaɗa kawai bata kara cewa komai ba, sai can ta nisa kana ta ce "Inaso naje Abujan naga yaran nan" "A wanne dalili? bazaki je ba, daga nan har abuja kawai dan kiga yara" "Alhaji ka..." "Na gama magana Saudat bazaki ba, za'ayi hutun karshan shekara kinsan kuma nan suke hutun ko wanne shekara, kamar yau ne fa" shuru Ammi tayi bata sake ce masa komai ba taci gaba da abinda takeyi, haka kurum inta tina Aimanah sai gabanta yai wata irin faɗuwa, hakan yasa ta yawaita kiran Aimanah a waya suna gaisawa kusan duk safiya saita kirata, tana tambayarta suna lafiya takan amsa mata da suna nan kalau hakan yasa hankalinta ya kwanta sai kawai take binsu da addu'a, SUMAYYA Cigaba tayi da jin daɗinta a gidan Mustapha nan da nan tai kiba ta zama katuwa masha Allah, Mustapha ko albashi ya ɗauka gaba ɗaya yake ɗebo su yazo ya juyewa Sumayya su tayi abinda ranta ke so, wani dankareran gini ta sa Mustapha yafara a kano can ɗan bare, gida ne na alfarma wanda taciwa buru daga an kammala ginin kano zata dawo taci gaba da zama, gidanta ya zama gidan mata kawayanta take tarawa na makaranta azo aci abinda rai keso wasuma har suyi guzuri banza ta faɗi, gidan ne gaba ɗaya ya hautsine da hayaniya yayin da wasu ke can gefe an kunna kiɗa ana casu da alama wani shagalin suke, Hajiya Hanne ta kalli Amarya tana fari da idanu take faɗin "Anya kuwa kin gane kwatamcan gidan nan da yarinyar ta maki?" "Haba na gane mana inaga wannan kwanar zamu sha" Amarya ta faɗa tana nunawa Hanne dake tuka motar kwanar da zasu yi, motoci birjik a kofar gidan da Amarya take tunanin shine na yarta Sumayya kamar yanda Murjana ta masu kwatance, kai tsaye scurity yabasu damar wucewa ganinsu gwagaggun wayayyun mata har wani risina masu yake yana kwasar gaisuwa ganin da ya masu jibga jifga da su daga gani nera ta zauna, Amarya saida gabanta yafaɗi ganin Sumayya cikin mata tana tikar rawa, zuciyarta tai wani tsalle kamar zata fasa kirjinta ta fito, saurin karasawa tayi ta katse kiɗan ganin yanda gaba ɗaya basu san an shigo ba hankalinsu nakan rawar da suke anata rungume rungume, leena ta kalli Amarya tana yamutsa fuska "Yada haka ne hajiya zaki zo ki rage mana jin daɗinmu" "Ke! mamana ce" Sumayya ta katse lina da sauri tana karasowa gaban mama ta ruko hannunta ta mata mazauni nan kan kujera, Hajiya Hanne wani kallo tabi Leena da shi tana latsar leɓe, Mama na ankare da ita hakan yasa ta ɓata fuska sosai ta hau sumayya da faɗan ta tara mata a gida anata rawa maye hakan kamar a kauye, "Mama kawaye na ne fa na school murna suke tayani na cikar wani buri nawa" "To su bamu wari" mikewa sukai yayin da Hanne ke magana da lina ta idanu dan ta lura itama yar hannu ce, gidan tsit yayi daga Sumayya mama sai ko Hanne "Naji gidan yayi shuru kuma ina kishiyar taki da yaran nata naji ance ta haifi yan uku ko?" Sumayya gyara zama tayi tana kallon Maman nata ta fara bata labarin abinda tayiwa Aimanah "Da kyau Sumayya gado ba karambani ba, ko ke fa har kin wanke min zuciyata da bakin takaicin danake ciki na waccan yarinyar Murja, naji daɗin wannan lamari, amma a ina wannan bokan yake da kin kaimu munje mun gansa kan wasu bukatu namu" "Mama bafa boka bane malam ne" "Duk kanwar ja ce Sumayya yaushe zaki rakamu" "Mama sai dai gobe yau yamma tayi kuma kinga akwai j nisa idam muka tafi yanzu ba lalle muje yau bama" "Yau da goben ai duk ɗaya ne Sumy Allah ya nuna mana" Hanne kallon Amarya tayi "Nan zaki zauna ne ko tare zamu koma hotal" "Ki koma kawai ni ina nan goben dai ki fito da wuri sai mu wuce saura kuma ki nemi wata idan kikai haka ban yafe ba" dariya Hanne tayi ta fita batace komai ba, Hanne na fita ta hau dube dube kamar mai neman abu, ji tayi an rungumeta ta baya ana shafarta jiyowa tayi sukai ido huɗu da Leena dake wani karairaya tana juya idanu "Hotal zamuje ko kinada gidan da zamu je" "Muje gidana mijina baya nan yara ma duka sun tafi tare garinsu" "Yawwa naji daɗin hakan" A motar hanne suka tafi daman Lina batazo da mota ba tare sukazo a motar feenah, finar kuma ta wuce, "Mama wai har yanzu kina tareda matar nan baki koma katsina ba, mama kibar harkar nan kiyi aure kawai" "Aure a wannan lamarin Sumayya nadai kusa barin harkar nan zan tuba ga Allah na koma gaban iyaye na na kama kasuwanci ni yanzu maza basa gabana ko sha'awa ma basa bani, wai wanna yarinyar mai tsayayyun idanuwa ina kika samota" "Wa kenan?" Sumayya ta faɗa tana dariya, Amarya kwatanta mata ita ta hau yi nan take Sumayya ta gano Lina Mama ke nufi "Ki bita a hankali, na fuskance ta yar maɗigo ce" "Mama" Sumayya ta faɗa hannunta saman kirjinta alamar tashin hankali "Tabbas gaskiyya na faɗa maki yanzu haka bana ɗebe shakkun suna tare da Hanne dan naga sunyi magana da idanunsu basu zaci na gansu ba," gumi ne yafara zubowa Sumayya tana gogewa da hannunta wani iri take ji a zuciyarta nan take tsoron Lina ya shige ta dan ita kam matsoraciya ce musamman akan irin wannan harkar, tun adaran taɗau aniyar zata ja baya da lina tabbas, Amarya anan gidan ta kwana washe gari sassafe suka ɗau hanyar enugu. Murjana tsaye tana kallon Alhaji Jamil dake zazzaga masifa kamar ba shi ba tun iya tsawon zamanta a gidan bata taɓa ganin yana masifa irin haka ba, bata taɓa zaton yanada zafi ba sai yau da Uwar gidanta ta taɓo sa "Dan Allah Abban Jannat kayi hakuri kuskure ne Maman Jannat ta riga tayi kuma tun farko da laifinka tunda kai kabata damar yin komai" "Ke yarinya shiga hankalinki karki sake shiga maganar mata da miji" "Rahila ki kiyaye ni ba ruwanki da yarinyar nan ke yanzu bakiji kunya ba, yaushe rabonki da zama ki kula da yaranki mai zaki iya faɗa na halin yaranki tunda yarinyar nan ta shigo gidan nan gaba ɗaya kulawar yaran ta dawo kanta ko yaushe tana hidimarsu ke kuma kin maida kai wajan yawon koyarwar ki da tara mata da kike masu sarin kaya, to daga yau na soke karna sake ganin kafar ko wacce mata a gidana idan na kuma gani wallahi saina masifar saɓa maki" yana gama faɗar haka yasa kai ya koma sashin sa "Kinyi nasara ki karawa bokanki kuɗi yau Abban Jannat yamin abinda bai taɓa yimin ba, zanyi maganinki ni nafiki tantiranci banbancinmu ɗaya ni ban taɓa bin maza ba balle nayi cikin shegen da agarin cire sa na rasa mahaifa" Murjana da sauri ta ɗago ta kalli kishiyar tata nan take kuka yazo mata najin abinda ta faɗa da gudu ta wuce sashin mijinsu ta faɗa gado ta fashe da kukan nadama, ina matar nan taji wannan labarin datake bunnewa bayan daga yayunta maza ba wanda yasani sai Alhaji Jamil kawai da ta faɗawa jikin Murjana yai sanyi taji a ranta Alhaji Jamil shiya gayawa matar sa maganar, Alhaji Jamil daya fito daga wanka ya kalli Murjana dake matsanancin kuka tuwul ɗin hannunsa ya ajje ya zauna kusada ita ya ɗago ta ya haɗa ta da jikinsa "Murja maiya faru maiya saki kukan nan?" "Zaka ce haka mana tunda ka kwashe sirrina ka gayawa matarka sirrin dakasan ina matukar ɓoye sa" "Maina gaya mata ni ban taɓa gaya mata komai ba ki yarda dani yaushe ma na zauna da ita da har zan gaya mata wata magana" "Zakace bakai ka gaya mata anciremin mahaifa ba sannadin aborsion" "Zan iya rantse maki da Allah bani na gaya mata ba, amma zo muje ki ji gaskiyya daga bakinta" hannunta ya ruko suka je har ɓangaran Maman jannart, Alhaji Jamil ya kalli maman Jannart kallon da Murjana ta kasa gano kona mene, shin naso ne ko kuma na gargaɗi "Ki faɗi tsakaninki da Allah Rahila nina faɗa maki wannan maganar" dariyar shakiyanci Rahila tayi tana kallon cikin idanun Mijin nasu ta ce "Alhaji so kake na karyata kaina a gaban yarinya nace karya nayi, nan nan kazo kana faɗamin kawai zaka auri murja ne sabida hutawa aiba haihuwa take ba mahaifarma an cire ta sakamakon cikin shegen da tayi aka zubar har kace na saki raina Murja zuwa zatayi ta tayani rainon ƴa'ƴa na tunda ita batada mahaifar da zata ɗauki cikima bare harta haihu kai nawa ne daga ni sai yarana harka manta ranar kenan?" Murja kuma rushewa tayi da kuka ta fice, ɓangaranta ta koma ta ci gaba da kuka, Alhaji Jamil kasa motsi yayi daga inda yake zaune yana kallon Rahila da har sannan dariya take kamar wacce tasami matsalar kwakwalwa "Rahila ni kika yiwa sharri? yau she mukayi haka dake?" "Sam bamuyi haka da kai ba, nayi ne danna ɓata maka kuma ba'a wajanka naji wannan labarin ba a duniya na jiyo" numfashi Jamil ya sauke sannan yasami kwarin gwiwar barin ɗakin ya koma nasa ya gyara jikinsa sannan ya shiga ɓangaran Murjana barci take da alama tana kukan barci ɓarawo ya yi gaba da ita, sumbatarta yayi kana yasa kai yafita daga gidan zuwa kasuwa, Murjana fushi ta ɗauka sosai da Alhaji ranar ko girki batayi ba kamar yanda tasaba takan bawa driver na gidan yakai masa kasuwa, Alhaji Jamil ma ganin time na kawo abinci ya wuce ba'a kawo ba yasa ya kira ta a waya lokacin futowarta kenan daga wanka tana ganin kiran harya katse bata ɗaga ba sabida ta shaka da yawa da abinda ya mata tagama sawa a zyciyarta inya dawo zata nemi ya sawwake mata ta kama gabanta tayi nisa da gari can tayi wani auran inda baza a san maita aikata a baya ba, zuciyarta ce ta kuma rauni hawaye ta soma sharewa tana sake nadamar abinda ta aikata a baya taci gaba da istigifari da jin tsananin tsanar mahaifiyarta Amarya da Salim da kuma ruɗi da kuruwar sheɗan da tabi yanzu gashi ta kaita kogin nadama, shikenan ita batada rabon ganin ɗanta shikenan ita da haihuwa sai dai ta gani anayi, Jannart ce ta shigo tana gudu waya kange a kunnan ta "Momy ga Abba yace na kawo maki waya zakuyi magana" "Bar nan Jannart fita bana son ganinki bazan amshi wayar ba bazan amsa ba ɗin" tafaɗa tareda fashewa da kuka "Abba Momy taki karɓar wayar kuka ma take yi" Jannart ta faɗa tana tsaye daga inda take, Alhaji Jamil katse kiran yayi ko Jannart bata gaya masa ba yariga yaji kukan nata hakan yasa ya mike yabaro kasuwar zuwa gida, Jannart kasa futa tayi jiki sanyaye ta karaso kusa da Murjana ta tsugunna "Momy mai aka maki kike kuka kiyi hakuri ki shuru mom" "Jannart fita! ki fita kafin na saɓa maki" Jannart yarinya yar shekara goma yarinya mai hankali da nutsuwa komai nata a nutse take yi cikin sanyi ta ce "Mom vazan iya fita na barki kina kuka ba, muma fa kin hanamu kuka kina mana duk abinda muke so mom ta yaya zan futa na barki kina kuka" Murja ɗagowa tayi ta kalli yarinya ta ruko hannunta taci gaba da kukanta, a haka Alhaji Jamil ya shigo yasame su ya kalli Jannart yabata umarnin ta fita ta futa kuwa tana waigan Momy ɗinsu "Murja wai baki daina kukan nan ba har yanzu dan Allah kibar kuka haka" "Bazan bari ba, nace bazan daina ba, ka sakeni Jamil kasake ni naje na auri wani wanda baisan sirrina ba bare ya gayawa matarsa sirrina, nayi nadama nai nadamar auranka da nayi" "Ni kuma banyi nadama ba bazan kuma taɓa nadamar auranki da nai ba, a yanzu ko anan gaba kowa da kaddararsa Murja ni ban taɓa gayawa Rahila magana makamancin haka ba ke maca ce kinsan tuggu da kissa irin taku ta mata, tabbas ita rahila ta maki sabida tana bakin cikin zaman lafiyar da muke da ke, kima ɗauka ana faɗa mata na yarda na faɗa ɗin duk da nasan ban faɗa ba amma na karɓi laifin indai zuciyarki zata yi fari kiyi hakuri, bana son ɓacin ranki sarauniyata haka my zumata yi murmushi mana" Murjana ɓoye fuskarta tayi a kirjin Alhaji Jamil tana murmushin kamar yanda ya umarce ta "Ko kefa masoyiya idan irin haka ta faru tsakaninki da Maman Jannart ki nuna mata bakiji hau shi ba ki kuma daina kuka a gabanta zata raina ki" kai kurum Murjana ta ɗaga batace masa komai ba, kasuwar da bai koma ba kenan ya zauna faranta mata daga nan suka lula duniyar maji daɗi🚶‍♀️ Abbas Home Kuka take kasa kasa, yayin da Abbas ke rungume da Usaina yana jijjigata dan itama kukan take tsan yarawa, Hassan ne kwance cikin net ɗinsa yana wasa, kallo ɗaya yayiwa Rumana dake kuka ya ɗauke kansa duk da kuwa har cikin zuciyarsa yake jin kukan, da kyar yasamu usaina ta daina kukan tai barci net ɗinta ya buɗe yasata yana mata addu'ar kwanciya barci, sake kallon Rumana yayi data karo sautin kukan nata ya matso kusa da ita "Yi shuru to naji za'a zubar da cikin amma nima zaki bani dama na kara aure na auro mai sona wacce bazata gaji ba wajan haifa min ya'ya" "Nima ai ba gajiyawa nayi ba, kawai ina tausayin su twince ne duka duka watansu shida fa kuma ace ina ɗauke da cikin wata uku ai da tausayi yaya za'ayi da su?" "Amma ca nake a gabanki Dr yace ba damuwa indai za'a basu kulawa kuma za'abi dokoki a kiyaye su zasu kasance cikin koshin lafiya" "Amma Hayatie duka nono na shekara ɗaya fa zasu sha kenan" "To maye a ciki, Allah kawai ya raya su" "Nidai wallahi bazan yarda ba yazama dole a zubar da cikin nan ko kana so ko baka so ni saina ɓarar da shi" mikewa Abbas yayi yafita daga ɗakin ransa ɓace, wayar Ammi ya kira bayan sun gaisa ya ɗanyi shuru kamar bazaice komai ba har sai da yaji Ammi na faɗin "Hello Abbas kana kan layi?" "Ina nan Ammi, daman wata yar matsala ce ta taso Rumana ce batada lafiya, jiya munje hospital likita ya tabbatar mana tana ɗauke da cikin wata uku, tun safe yau take ta kuka wai sai an zubar da cikin, na lallasheta taki ganewa yanzu tace ko ban yarda ba wallahi ita saita zubar da shi, Ammi inason haihuwa ni kaɗai iyaye na suka haifa zanyi farin ciki idan naga nima na tara iyali da yawa" "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un ita Rumanar zata aikata wannan babban zunubin ina fatan kana gidan?" bata jira amsar saba taci gaba da maganarta "idan kana ciki ka zauna ko nan da can karka motsa ka saka mata idanu sosai ni kuma ka bani awanni uku zan shigo abujan bari nasa Ahmad yasai min ticket Allah yasa akwai jirgin da zai zo nan yanzu zan taho insha Allah ka kula sosai" "Insha Allah Ammi amma dan Allah karki faɗawa Anty kinsan yanzu taji labarin nan hankalinta zai ta shi ta ɗagawa kowa hankali" Ammi dariya tayi kana ta ce "Hasana kenan kaima kasan wannan halin nata, bazan gaya mata ba kaima kai shuru da maganar dan Allah ko hajiyarka karka faɗawa" "Insha Allah Ammi sai kinzo" juyawa yayi ya koma ciki yayin da ita kuma Ammi ta wuce sashin Alhaji Kamal wanda akai katari yana gidan bai futa kasuwa ba, bai mata musu ba sanda ta faɗi abinda ke faruwa nan take yasa aka sai mata ticket na tafiya Abuja AIMANAH Islam taji sauki sosai ta murmure, bayan tasha allurai da magunguna yau Aimanah tun safe take aikin bauta sai ɗorawa da saukewa take na kawayan Sumayya da suka cika gidan ko wacce kuma da kalar abinda zata ce ayi mata, Lina duk wani motsin Aimanah idanunta na kai har zuwa yanzu da Aimanah ta kawo masu soyayyar taliyar data gama yanzu "Kai nifa bazanci taliyar nan ba, inaga ko indomie za'a dafa min" feenah ta faɗi haka tana kallon Aimanah wacce sam bata iya ko yi masu musu duk abinda suka ce aiwatarwa kawai take "Ba wani indomie da zata dafa maki in bazaki ci wannan ba ki bar shi" Lina tafaɗa a zafafe, feena wani kallo ta mata ta ɗauke kai tana murmushi "Ke Aimanah jeki ki huta kuma ki ɗebi yanda zai isheki keda yaran" juyuwa Aimanah tayi ta koma kicin ɗin "Gaskiyya kawarmu abinda kikewa kishiyarki yayi yawa tunda kin riga kin farraka tsakaninta da mijinki ki barta mana ta huta gara ma kisa ya rubuta mata takardar saki ta bar maki gidanki ki huta" "Gane min hanya dai Faty da sanda muka tallata mata abin nan kamar ta kirki sai da muka sha fama ta amince mukaje enugu amma yanzu harta zarta mu wajan mugunta" "Sumy dan Allah ki maido da yarinyar nan wajan nan canfa ba daɗi kinsan yanda wajan nan yake ga yara" ca ɗin da kawayan Sumy sukai mata shiyasa ta sa Aimanah ta dawo ɗakinta itada yaranta, Lina har ɗaki tabi Aimanah ta taya ta gyara ɗakin "Ammi karfe biyu na rana ta shigo Abuja, Abas yaje ya ɗakkota, Rumana tana ganin Ammi da Abbas tasha jinin jikinta musamman irin kallo da taga Ammin na mata ko zama batayi ba tafar aikawa Rumana faɗa Ammi ba baya ba wajan faɗa da musamman inka ɓata mata rai, Rumana jikinta yayi sanyi da faɗan da Ammi ta mata sai sannan taga wautarta shekarunsu huɗu da aure sanan ta haihu yanzu kuma ga wata kyautar daga Allah cikin kan kanin lokaci amma tana neman bin hudubar sheɗan ta butulce ma Allah, tana kuka sosai tabawa Ammi hakuri sannan ta nemi Abbas daya yafe mata, da kyar ta lallashi Ammi ta zauna taci abinci ta umarci Abbas daya kaita gidan Aimanah su gaisa ba zama zatayi ba jirgin karfe huɗu zata bi ta koma kano, Aimanah na tsaye tana mooping anan falo aka turo kofa aka shigo, tsallan murna tayi tana ɗane Ammi gaba ɗaya yaran sukayo kanta suna ihun ganin Ammi, Ammi zama tayi kan kujera tana kafe Aimanah da idanu ko gaisuwar da Aimanah take mata bata amsa ba saima tambayya data aikawa Aimanah "Aimanah lafiyarki kalau kuwa naga kunyi rama gaba ɗayanku keda yaran?" murmushin yake tayi batace komai ba tai kasa da idanunta hawaye na zubo mata ta buɗi baki zata gayawa Ammi halin da suke ciki amma ta kasa bakinta ya mata nauyi maimakon ta faɗi abinda ke cikin zuciyarta sai taji bakinta ya furta saɓanin abinda ke zuciyarta ahankali ta ce "Ammi muna lafiya kalau, munyi fama da zazzaɓi ne gaba ɗayanmu musamman Islam" Ammi dake rungume da Islam tana shafa kanta ta ce "Gidan shuru Sumayya bata nan? daman nasan Mustapha yanzu yana office jiya ya kirani mun gaisa ya gaya min abubuwa suka masa yawa shiyasa kwana biyu bakuje kano ba" Kai kurum Aimanah ta ɗaga zuciyarta fal zulumi da tunani yanda zatayi da Ammi tun jiya da yamma Mustapha da Sumayya suka fita basu dawo ba sumayya ta kulle store suma Maman Hanif ke aiko masu da abinci, mikewa tayi ta shiga ɗakinta jiki na rawa ta kira Maman Hanif ta gaya mata Ammi tazo, "Gani nan zuwa" maman hanif tace Aimanah ta fito falo wajan Ammi da suke magana da yaran, Maman Hanif ta shigo da katon hijab ɗinta fuskarta da murmushi suka gaisa da Ammi, Ammin na tambayarta yara "Maman Aslam baki kawo wa Ammi abinci ba" "Nama manta gaba ɗaya ɗokin ganinta ya mantar dani ana kawowa bako abinci da ruwa" "Bari to nashiga kicin ɗin na ɗora mata ko macaroni ne" "A'a Maman Hanif bazan ci komai ba adai kawo min lemu da ruwa amma na koshi da abincin nan naci gidan Rumana" maman Hanif ta shiga kicin mintina kaɗan ta fito hannunta ɗauke da plate mai ɗauke da goran ruwa dana lemu, lumshe idanu Aimanah tayi tana jin wani sanyi a zuciyarta "Ammi gashi, kinga Aimanah duk ta rame jinya tayi sosai har kwana biyu mukayi a hospital Musty ya hana a sanar maku kada hankalinku yata shi" Ammi na murmushi ta ce "Allah ya kara lafiya" har sannan idanunta nakan Aimanah kamar mai irga kashin wuyan ta, mamaki matuka take na ramar da Aimanah tayi tabbas yazama dole ta bincika mai ya saka Aimanah haka wannan rama ko kusa ko alama bata yarda Aimanah jinya tayi ba, tadaifi zaton akwai abinda Aimanah da Maman Hanif suke ɓoye mata, bata wani jima can ba sanin Abas na waje yana jiranta yasa ta mike "Zan tafi Aimanah idan abokiyat zamanki tazo ki gaidata da mai gidan" har bakin get Aimanah ta mata rakiya "Aimanah ga Abbas can ki fito ku gaisa" Aimanah nasa kafarta a bakin kofa taji kamar wacce aka saka mata shoking na nepa da sauri tayi baya har tana shirin faɗuwa "Subhanallah sannu bi ahankali Aimanah" Ammi tafaɗa cikin kulawa "Ammi ki gaida gida bazan iya zuwa mu gaisa da Abbas ba" da sauri ta juya zuwa ciki sabida har sannan bataji jikinta ya koma dai dai ba, saman kujera ta zauna jikinta na rawa sosai ji take ana sake ɗaure mata jiki wata kara ta saki bata sake sanin inda kanta yake ba....✍🏻 [2/13, 4:46 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi Na Talatin da uku* Sumayya dake tsugunne gaban malam, baya tayi zata faɗi ganin Aimanah ta bayyana a gabanta gata nan muraran kwance kan kujera kamar mai rai kamar mara numfashi, ga Maman Hanif nan a gefanta tana faman mata fifita, "Ran Malam yadaɗe ban gane ba, kar dai kace min ta mutu?" Sumayya ta tambaya hankali tashe "Hhhhhhhhhhhhh, bata mutu ba, saura kiris saura kiris aikinki ya tarwatse yau, wacece wannan?" malam yafaɗa yana nuna mata wani kasko dake gabansa Ammi ce ta bayyana zaune cikin jirgi, "Su ru ka ta ce" Sumayya ta faɗa a rarrabe, Ammi gyara zamanta tayi cikin jirgin tareda ɗago da hannunta ta fara tasbihi, wani feshin wuta ne yata shi daya kusa kama fuskar Sumayya data kurawa Ammi idanu "Zata ɓata mana aiki wannan matar tanada karfin ibada bata inda zamu ci galaba a kanta, tabar gidanki da kudurin binciko abinda yasa kishiyarki da yaranta rama ko mai zai iya tarwatsewa aduk randa ta sake shigowa gidanki" "Malam ayi wani abin dan Alah, bana so na rasa wannan damar so nake na rayu a haka har karshan numfashi na" "Wiiiiihuuuuuuuhuuuuuu, zamuyi zamuyi zamuyiiiiiiii" yafaɗa da wani irin ihun dayasa Sumayya yin baya sosai da shi "Nasa Aljani dundurusu yayi komai, zaki biya mu kuɗin aikin mu sannan aljani ɗan jani zai biya bukatarsa da ke," zaro idanu Sumayya tayi tsoro yasake mamaye zuciyarta aljani kuma yanzu aljani ne zai biya bukatarsa da ita, bata gama tunanin ba taji kamar ana shafarta bata sake sanin inda kanta yake ba, sai farkawa tayi ta ganta kwance a ɗakinta, wani tsalle ta buga tareda sakin ihu, dai dai nan Aimanah ta saki wani numfashi Maman Hanif ta ce "Alhamdulillah Allah mun gode maka, sannu Aimanah" "Yawwa" Aimanah tace a sanyaye, gaba ɗayansu tsorata sukayi sanda sukaga Sumayya da rabonta da gidan tun jiya fitowa tayi daga ɗakinta, cikeda mamaki Maman Hanif ke kallon Sumayya ita dai tana nan falon tun sanda Aimanah ta suma bata bar falon ba bare ta ce anan Sumayya ta shigo amma abin mamaki sai gata daga ɗakinta, mintina kaɗan kuma sai ga shigowar motar Mustapha "Sannu maman Aslam ya kike jin jikin" "Da sauki sai dai kaina ji nake kamar ba nawa ba" "Sannu shima zai daina kici gaba da ambaton Allah" sallama Maman Hanif taiwa Aimanah ta fita, Aimanah ma ɗakinta ta shiga sai dai ko zama batayi ba sai ga Sumayya a ɗakin, tsaye tayi jikin kofa tana girgiza jiki "Kizo ki wankewa Mijina mota" haka kawai tafaɗa ta fita daga ɗakin, jikin Aimanah yana rawa tabi bayan ta sabida wani tsananin tsoronta da ta ji ya kara shigarta fiye dana da, motar tayi datti sosai jikin tayar motar futu futu da jar kasar da alama motar wajan gari akaje da ita, tanayi tana haki ga sanyin ruwa haka ta gama abinda bata taɓa yi ba, tanayi tana goge hawayen takaici, Sumayya na gefe ta kafa kujera tana kallon Aimanah tana mata dariya da wake waken habaici, Aimanah data koma dakinta kuka ta sha sosai daran ranar batai barci ba raya daran tayi da nafiloli tana kuka tana gayawa Allah halin datake ciki, washe gari sarai ta tashi zuciyarta fes har wani nishaɗi take ji, kasancewar da azumin nafila ranar ta ta shi, abincin da Maman Hanif ta aiko masu da shi gaba ɗaya taba yaran suka cinye duka matukar tausayin yaran take zuwa yanzu yaci ace suna aji suna ɗaukar darasi amma ga yanda rayuwa tayi da su hakan yasa ta bada kaimi wajan addu'ar Allah yafitar da ita daga wannan hali datake ciki, wayar hannunta ma Sumayya ta karɓe ta a gabanta ta bugata da kasa sabida kawai ta ganta suna waya da maman hanif. GIDAN MURJA Alhaji Jamil da yaransa uku Jannart Labiba da Ansar zaune bisa danning, yayinda Murjana keta zuruftu daga kicin zuwa danning area ɗin sai da ta gama ajje komai kana ta zauna, kallon yaran tayi da murmushi a fuskarta ta ce "Baza kumin sannu ba" lokaci ɗaya suka haɗa baki suna faɗin "Momy sannu da aiki" dariya tayi tana kallon Alhajin daya ke ɓata fuska kamar wani karamin yaro "Kaifa Man wani bin in kana abu sai kace Ansar" ta faɗa da murya kasa kasa, "Inajin yunwa sosai, yau banci abinci a kasuwa ba" da sauri taja plate ta soma zuba masa abincin farar shinkafa ce sai farar doya da miya, sai haɗin salad gabansa ta ajje plate tana faɗin "Bisimillah" kansa ya ɗora saman kafaɗarta murya kasa kasa ya ce "Nifa ke zaki bani" "Yara na nan fa" itama ta faɗa a hankali "Ki basu nasu su wuce wajan mamansu suci acan" "Kasandai ba sakewa zasuyi a can ba ga nanny bata nan kawai dai ka daure kici da kanka" mikewa yayi zai bar wajan tasa hannu ta ruko sa "Jannart zubawa kowa abinci a plate kuci" ga lemu nan kowa ya ɗau wanda yake so amma Ansar kar abasa mai sanyi" taɓe fuska Ansar yayi kamar zaiyi kuka murja taja kumatunsa tana murmushi ta ɗauki plate ɗin data zubawa Alhaji abinci suka zauna can falo ahankali take basa abinci a baki yanata zuba mata shagwaɓa kamar wani karamin yaro, saida ta tabbatar ya ishe sa sannan taci kaɗan, ta koma wajan yaran data soma jiyo hayaniyar su "To yaya ne, zaku fara faɗan ko?" "Momy Ansar ne fa wai sai ya sha lemu mai sanyi kuma kin hana abasa sabida yana mura" "Naji ku wuce to Jannart ki tabbatar kin tayasu sunyi homework ke kinga munyi naki ɗazu in kun gama ku kwanta barci zan shigo ɗakin kowa yayi addu'a ku kuma kunna karatu a mp na ɗakin ku kisa bakara" kai Jannart ta ɗaga alamar to har sun soma tafiya suka jiyo suna mata bye bye Ansar da gudu yadawo ya rungumeta ya sumbaci kuncinta ya ce "Goodnight Mom" Murmushi Murjana tayi tana kallon yaron da yayi gaba da gudu, hawayan dake zuba a kuncinta taji ana share mata ko tantama batayi ba tasan Alhaji Jamil ne hakan yasa ta faɗa jikinsa ta fashe da kuka "Shikenan banda rabon ganin ɗana a duniya shi kenan bazan sami soyayyar da yara ke wa uwarsu ba? shikenan bazan taɓa haihuwa ba har abada? bazan sami ɗan da zai kula dani ba bayan na tsufa, kaicona kaicona nayi nadama Allah na tuba ka yafemin, Allah kabani hakuri da juriyar cin wannan jarabawar da kamin ya Allah" sosai take kuka mai taɓa zuciya, Alhaji Jamil ma hawaye ya share yana buga bayanta a hankali alamar lallashi "Yi shuru Wife dan Allah ki daina kukan nan gasu Ansar nan insha Allah zasu maki dukkan wani abu da ɗa kewa uwa" bata tsaya sauraron saba taci kukanta ta koshi yanata aikin lallashi, sai da tai shuru suka wuce ɗakinsa har sunyi shirin kwanciya ya ce "Mako guda ya rage fa tafiyarmu India" "Bazani ba, ka tina yanda akayi a tafiyarmu indunusia irin tashin hankalin da akayi da matarka dan haka wannan karon ka tafi da ita ni ina nan zan kula da yara" wani kallo yamata kana ya ce "Bazani da itan ba, dake naga damar tafiya kuma da ke zan tafi" jiki sanyaye Murjana ta kalli Alhaji daya kwanta ya juya mata baya agogo ta kalla taga tara saura minti biyar na dare "Gaskiyya Abban Ansar ba haka ake ba, yanda na sani in anyi tafiya da wannan in wata tafiyar tazo da waccan za'a tafi sai dai in ita tace ta yafe a tafi da wata" afusace ya mike yaja hannun Murjana zuwa sashin Rahila, kofar ya buɗe a fusace falon shuru ba kowa hakan yabasa damar buɗe kofar bedroom ɗinta, abinda yagani ya masifar ɗaga masa hankali bama shi kaɗai ba har Murjana wacce ta zaro idanu tana salati, salatin da Murjana tayi shiya dawo da Rahila da Hanne hayyacinsu da sauri suka ja bargo suka rufa, Rahila na zare idanu ganin Alhaji Jamil tsaye kamar wani sakago ya saki baki yana kallon su da kyar ya iya saita kansa ya ce "Daman abinda kike aikatawa kenan shiyasa kike tara mata a gidana, kike kin bina wani waje ina can na saki baki ashe ke ga abinda kike aikatawa, kin cuci kanki Rahila keda Allah kin aikata babban zunubi Rahila kije dan kanki na sake ki saki uku bake ba yarana na haramta miki su har abada ki nesa da gidan nan ki nemi inda zaki" juyawa yayi ya fita yanajin sa wani saroro kamar iska zata ɗaga sa sama, kuka ya sha sosai daran ranar, Murjana ko ɗakinsa bata koma ba ɗakinta ta koma itama ta sha nata kukan takaicin wannan zamanin da mata suka lalace, Rahila sanda Alhaji Jamil ya furta mata kalmar saki ba karamin tashin hankali ta shiga ba fiye dana ganinta da yayi kwance da wata hakan yasa ta fashe da kuka, shikenan ta kare mata ina zata iyayanta gaba ɗaya sun rusu da gidan Alhaji jamil ta dogara sai kuma aikin datake wanda bata wani tara abin arziki ba "Ki daina kukan nan dama ma yabaki yanda zaki sakata ki wala kiyi harka yanda ranki ya ke so munada kungiya ta mata yan less zamu saka ki a ciki zaki samu kuɗaɗe sosai zaki fantama mota sai wacce ranki yakeso akwai alhazan birni zaki iya auran ɗaya daga ciki wanda shi ba mace bace a gabansa shima yanada tasa harkar a gabansa ma zaki iya yin duk abinda ranki yaso da mace bazai ce maki komai ba si dai kawai yayi aure ne dan kada a zargesa in anga yana zaune ba aure, gobe ne ma zamuyi taronmu na shekara a kaduna ki zo mu tafi gidana inada mata kala kala acan da suke zaune" Rahila mikewa tayi ta sitirta jikinta ko wanka ba wanda yayi haka suka bursuna kaya suka fita a gidan a motar Rahilan, Amarya rai ta ɓata ganin Hajiya Hanne data ce mata taje jigawa sai gobe zata dawo, amma sai gata yanzu da tsohon daran nan harda guzurin wata matar "Daman wai ba jigawar kika tafi ba?" "Naje daga can ma nasamo mana wannan" "Ko dai kikaje wajanta ba, waton ni kin barni a nan kika ajje ni kin hanani holewa da kowa kince ni taki ce ke kuma kina bin wasu, nan haka da mukaje habuja gidan Sumayya daga ganin wata sai da kika bita kika kwana da ita, to gaskiyya nima fita zan na hole yanda raina ke so" "zaki iya yin hakan ai" Hanne tafaɗa tareda jan hannun Rahila sukai sama, saroro amarya tabisu da kallon mamaki can kuma tayi kwafa ta koma ɗakinta, Lumshe ido yayi tareda buɗesu lokaci ɗaya ya saki murmushi, ya buɗe kofofin hancinsa yana jin kamshin kasar sa da ya kwashe shekaru biyar cif baya cikinta ahankali kamar baya so ya ce "Nayi kewarki kasata, ina son kasata" zama yayi zaman jiran jirgin da zai kaisa tashi nan da minti arba'in da biyar zuwa kano "Yaya Aimah" yafaɗa a hankali sake kallon agogon da ke ɗaure a tsintsiyar hannunsa yayi still dai yanada saura mintina arba'in da uku kafin tashin jirgin da zai kaisa kano, mikewa yayi ya saɓa jakarsa a baya ya gyara zaman sun glass ɗin dake idanunsa ya fito zuwa waje inda masu texzii suke, "Barka da safiya Baba" Shaheed yafaɗa sanda yakarasa gaban wani tsoho mai texzii "Barka dai ɗana an sauka lafiya, ina zan ajje ka" faɗa masa sunan unguwar da Mustapha da Aimanah ke zaune yayi kana bayan ya shiga gaban motar mutumin har ya fara tafiya Shaheed ya ce "Baba zamu iya zuwa nan da minti talatin mu dawo airport jirgin kano zanbi na karasa gida" "Zamu iya duk da akwai yar tazara amma inba daɗewa zakiyi ba a wajan har ma dawo bari na kara gudun motar" kwantar da kansa yayi saman seat na motar kamar wani mai barci, haka kawai yaji gabansa na faɗuwa yayinda suka kusa zuwa unguwar ya buɗe idanunsa da suka soma canza kala "Yaya Aimah" yafaɗa a hankali, "Munzo ranka ya daɗe" Baice komai ba ya buɗe murfin motar ya fita yana kallon tangameman gidan dayake zaton nan ne inda yazo, jakar sa ya ajje a bayan motar yana kallon mutumin mai tasi ya ce "Baba bari na shiga bazan jima ba yanzu zan fito gidan yayata ne gaisawa kawai zamuyi" "Afito lafiya" sa kai yayi zai shiga get man ya tare basa kofa "Daga ina" "Daga gidan uwarka, dalla gyara ka bani waje na shige kasan koni waye a gidan nan zaka tare min hanya," hannu yasa ya wurgasa can gefe ya shiga ciki yana huci Aimanah na rike da Islam wacce ke kukan yunwa yau yini biyu kenan basu saka komai a bakinsu ba, bata san ya akai ba Maman Hanif jiya da yau duka bata shigo ba gashi ita kuma ba waya a hannunta, sallamar da taji yasata ɗago da sauri ta kalli wanda ke shigowa "Shaheed" ta faɗa a hankali yayinda idanunta ke kawo ruwan hawaye, da sauri ya karaso ya tsaya a kanta can kuma ya zube kan kafafunsa yana kallo Yayar tasa ba ko kiftawa "Yaya Aimah kece kece kuwa lafiyarki kalau cuta kika yi da kikai wannan ramar ina Yah Musty" "Shaheed abinci, yaran nan yunwa suke ji rabonsu da abinci tun jiya da safe" bai tsaya tambayar ba'asi ba ya mike ya juya ya fita mai motar daya kawosa ya bawa kuɗi ya ce yaje gidan abinci mafi kusa ya yo masa take away ya juya ya koma ciki "Yaya Aimah wai ina yayanmu" "Shaheed muna cikin matsala" karo na farko data buɗi baki ta iya gayawa wani halin datake ciki a gidan kuka sosai Shaheed keyi, kamar wani karamin yaro "Sannu yaya sannu yaya Aimah insha Allah saina fitta ki daga wannan halin, yanzu bazaki iya fita daga gidan nan ba, muje ki ga ya mike shiya taimaka mata tasa hijab ya ɗauki islam da jikinta ya saki sosai ga zafi da jikin yayi, ya ruko hannun Aslam da Tasnim cak taja ta tsaya lokacin da suka je bakin get "Shaheed gasu nan za su kashe ni, Shaheed mage ce gata can a kofar fita bazan fita ba katafi da yaran kaje ka sanar da halin da nake ciki, ga wasu nan zasu hanaku tafiya shaheed fita da sauri" hannu tasa ta tura su waje ta mai da kofar ta rufe gam, tana jin sanda Shaheed ke faman kwaɗa mata kira, zama tayi jikin get ɗin "Shaheed ka kai yaran nan wajan Ammi ku maza ku tafi kafin Sumayya ta dawo bazata bari ka tafi da su ba" Shaheed jiki a sanyaye ya saka yaran cikin motar data kawo sa a ciki ya basu abincin sukaci sosai har mamakin abincin da sukaci yake, ya kalli agogon hannunsa yaga jirgi tuni ya tashi kusan da mintina biyar kenan "Baba kaini tashar da zan sami motar da zata kaini kano" kai kurum baban ya gyaɗa yana cigaba da tukinsa har yakaisu ta sha kuɗi sosai Shaheed yabawa driver ɗin ya sami wata motar su kaɗai yabiya suka ɗau hanya, yana rungume da Islam wacce yakejin kaunar yarinyar ta daban data yan uwanta, Tasnim na gefansa na dama yayin da Aslam ke gefansa na hagu sun kwantar da kansu a jikinsa sunata barci, gafda zasu shiga kano Islam ta fara kelaya amai kamar zata amayar da hanjin cikinta jikinta ya ɗauki rawa idanunta na kafewa, gaba ɗaya hankalin Shaheed yatashi sai cewa mai motar yake "Dan Allah ka taka motar nan sosai mukai yarinyar nan hospital karta mace min" Aminu kano hospital suka je da wayar driver ɗin yayi amfani ya kira wayar Ammi, Ammi dake tsaye gama wayarta kenan da Ahmad wanda ke sanar mata jirage biyu kenan na sauka daga Abuja amma ba shaheed a ciki zai taho gida, gaba ɗaya hankalinta ya tashi tunani take maiya sami autan nata a yanda suka lissafa karfe sha ɗayan rana a kano zatai masa gashi yanzu magana ake ta huɗu harda kwata na yamma, jikinta ya kuma yin sanyi ta zurfafa cikin tunani har tsorata tayi sanda taji wayarta tayi kara, kamar bazata ɗaga ba ganin lamba ba suna sai kuma ta ɗaga sanda kira na biyu ya kuma shigowa wayar "Ammi ina hospital kiyi maza ki zo dan Allah" "Shaheed kana lafiya wanne asibitin maiya sameka yimin bayani" "Ammi ina lafiya, kizo dai nan Aminu kano" cikin ruɗewa ta fito, tareda Momy suka tafi bayan ta mata bayanin Shaheed ya kirata, Ahmad ta kira tace su haɗu a can Ammi duk gudun da Momy keyi da mota gani take kamar sanɗa take ta kagu taje taga maiya sami ɗanta, yana tsaye sanda suka karasa a wata farfajiya ko gama dai daita motar batayi ba Ammi ta fito tana taɓa Shaheed "Lafiya mai kake a hospital," baice komai ba yaja hannun Ammi suka shiga wani ɗaki, gaba ɗaya yaran suna kwance a gadajansu harsu Aslam yasa a binciki lafiyarsu "Ammi kuna kasar nan amma yaya Aimah na cikin wani hali ba wanda ke bin ta kanta kun mata adalci kuwa?" Ammi kanta ne ya sara tai saurin dafa kan tareda dafa bango Aimana tana turasu wajan get ɗin ta zauna wajan tareda fashewa da kuka wasu halittu ke mata gizo a idanunta kamar zararriya ta kwasa a guje ta shige gidan dan zamanta a wajan jitake kamar ana ɗaureta da igiya ɗakinta ta shige ta kwanta ta lulluɓa cikin blanket rufe idanu tayi har sannan tana hango haluttun nan na mata yawo cikin idanu buɗe idonta tayi tar wai tana karanto suratul bakara da karfin gaske, batayi nisa tana karantawa ba barci yayi awon gaba da ita tsawon awanni tana barci mai daɗi wanda ta jima batayi irin saba sai yamma sosai ta farka, durowa tayi daga gadon ta shiga bayi tai alwala ta tada sallah tai azahar kana tai la'asar tana nan zaune tana azkhair wanda ta jima sosai batayi ba taji an buɗe kofar ɗakinta, kallon kofar tayi Mustapha ne da Sumayya Musty na gaba rikeda takarda a hannunsa Aimanah ta kallesu kallo ɗaya ta ɗauke kanta har sanda taji Mustapha ya ajje mata takarda a gabanta "Ga shi Na sake ki saki ɗaya" lumshe idanu Aimanah tayi a zuciyarta take faɗin alhamdulillah, juyawa Musty yayi ya fita daga ɗakin, Sumayya ta kece da dariyar mugunta tana kallon Aimana "Yau dai mun yarda kwallon mangwaro mun huta da kuda, kici gaba da zama anan ke da yayanki nasan yunwa ce zatayi ajalinku, kina nan ba iya fita zakiyi a gidan nan ba sai sanda naso naga dama, kasar ma zamu bari zamu zaga duniya kafin mudawo nasan kin rigada kin zama ba matar Mustapha ba daga nan zan fitar dake daga wannan gidan" Sumayya ta fice tabar Aimanah saman darduma tana ambaton Allah da rokonsa akan yafitar da ita daga wannan ukubar da take ciki, zurawa takardar idanu tayi ta warwareta rubutun Mustapha raɗau saman farar takardar ninke ta tayi ta ajje ta saman gado, tana nan zaune ta jiyo futar su a mota bayan mintina taji an kuma shigowa ɗakin nata wannan karon Lina ce ta shigo ɗakin jikinta ne ya ɗauki mazari sam bata kauna ko san ganin wannan matar, wani kallo take bin Aimanah da shi kafin kuma ta ce "Zo muje," Aimanah ba musu ta mike tabi bayanta suka fito daga ɗakinta, ɗakin Sumayya taga sun shiga maida kofa lina tayi ta rufe batare data saka key ba, ɗaga katifar dake shimfiɗe saman katakon gadon Sumayya Lina tayi wata mage ta bayyana ramammiya da ita idanunta ja jawur da su ko kyan gani bata da "Kinason fita daga wannan halin da kike ciki, kinga wannan itace akayi asiri aka haɗa da ruhinki indai har magen nan na kulle anan bazaki taɓa iya barin gidan nan ba, ki bani dama da ƴan mintina na kashe kishi na dake ni kuma na maki alkawarin saina karya duk wani asiri da Sumayya ta maki," Aimanah baya taja ganin Lina na kokarin cire kayan jikinta, sai da lina tai tik ta ɗago tana kallon Aimanah dake makure jikin bango, jikinta gaba ɗaya karkarwa yake ambaton Allah kawai take a fili da zuciya, Lina ta tsugunna tana karkaɗa jiki a tunaninta zata ja hankalin Aimanah, kunce magen Lina tayi, cak Aimanah ta tsaya daga karkarwar da jikinta keyi, yanayin yanda take ji a jikinta taji gaba ɗaya ta sauya ta dawo Aimanar ta da, lokaci ɗaya taji kamar ana kunce ta daga ɗauri, juya idanunta kawai take a ɗaki tana neman abin dazata kare kanta daga Lina wacce ke kusanto ta, kan wata yar tukunya idanun Aimanah ya sauka batayi wata wata ba tasa hannu ta fusko tukunyar kasar ta bugawa Lina a fuskarta Lina ta saki wata karar azaba ta sheme anan, da gudu Aimanah ta fito daga ɗakin batayi wata wata ba ta fice daga gidan gaba ɗaya, gudu take sosai har batasan inda take jefa kafafunta ba sai ji tayi anyi sama da ita...✍🏻 07039793439 [2/13, 4:46 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi Na Talatin da Huɗu* ji kake keeeeeeeeeee matar dake jan motar tai saurin taka burki, Aimanah da motar tayi sama da ita ta dawo kasa kanta ya bugu da kwalta take yanke kan yafashe jini yafara zuba, nan da nan yan sanda dake kusa da wajan suka karaso ba'ayi wata wata ba akayi hospital da Aimanah wacce ko motsi batayi, matar data bige Aimanah kuka take sosai tana addu'ar Allah yatashi kafaɗun yarinyar data bige, hankali tashe ta kira babban ɗanta ta sanar da shi halin datake ciki, cikin kankanin lokaci sai ga shi a Hospital ɗin shiya rinka kwantar mata da hankali har zuwa sanda aka turo gadon da Aimanah ke kai daga emargency zuwa word, ruko hannun mahaifiyar tasa yayi suka bi gadon "Dr ya ake ciki" "Hajiya muje office na maki bayani" juyowa sukayi suka bisa zuwa office Muhd ya zaunar da mahaifiyarsa saman kujera ya tsaya jikin kujerar hannunsa cikin na maman nasa "Hajiya gaskiyya yarinyar nan na a cikin wani yanayi mara daɗi, ta bugu sosai a kanta a yanda muke tunani koda ta farka to zata manta komai nata, sai dai lamari na ubangiji komai na iya canzawa tsaɓanin binciken mu, a karshe dai muyi addu'a" "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un na shiga uku ni Zainabu yau kuma haka Allah yai dani kaico" "Mom please ki daina kiran shiga ukun nan komai zai zo da sauki insha Allah muyi addu'a kamar yanda Dr ya ce, Muje a kira Azinatu tazo ta kula da ita ke ki koma gida, mu kula da komai" "Muhd bazan iya komawa gida ba hankalina bazai kwanta ba tsoro nakeji karta mutu na shiga uku" "Mom zan kira Dr Fawas ya maki allurar barci fa kinsan yanayin ciwonki dan Allah ki cire damuwa, muje na taya ki kiyi alwala ki sallah kiyi addu'a Mom"jiki sanyaye ta mike tabi bayan ɗan nata Mustapha kwantar da kansa yayi jikin kujera, haka kurum yake jin jikinsa ba daɗi har wani zazzaɓi zazzaɓi yake jin na shirin kamasa "Sumy mu koma gida bazan iya tafiyar nan ba banida lafiya" harara ta wurga masa "Sabida kawai bakada lafiya zamu fasa tafiya holewarmu" mikewa yayi ya ajje mata takardunta a kan cinyarta ya mike zai bar wajan ganin da gaske tafiyar zaiyi yasa ta ji gabanta na bugawa tabbas wani abu na faruwa a gida, wayarta ce tayi kara alamar kira ne ya shigo zaro idanu tayi tana kallon Mustapha da har ya fita daga recepsion, hannunta na karkarwa ta ɗaga kiran Malam daya shugo wayarta "Kinyi sake, Lina ta ruguza komai harta tukunyar ki ta fasata" hannu Sumayya ta ɗora aka zata saki ihu ta tina a inda take cike da damuwa ta ce "Ran Malam yadaɗe yanzu yaya zanyi nasan dai tunda ina da kai banida sauran damuwa" "Komai ya rushe Sumayya, mijinki na gafda dawowa hankalinsa hakan dai dai yake da barinki gidan sa" "Shikenan na shiga uku ni Sumayya kayi wani abu dan Allah malam" "Zanyi akan mijinki Aljani shinzu zai shiga tunaninsa bazai dawo hankalinsa ba kafin muga mai zamuyi amma dai kisani komai ya rushe kishiyarki ta bar gidan, gobe ki shirin karɓar baki daga kano" yana gama faɗar haka ya katse kiran wayar, a mota ta tarar da Mustapha yana zaune da alama ita yake jira, tana shiga yaja motar suka bar aiport ɗin suna shiga gida ya kwanta barci ba sallah bare salati, zuciyar Sumayya tai sanyi ganin Mustapha baice komai ba ta daɗa kiran malam sukai waya ya gaya mata lalle jibi tazo a sake wani aikin akan Mijinta, gyara ɗakin nata tayi ta kwashe komai sama ko kasa ta duba magen nan bata ganta ba, rai ɓace ta nufi gidan Lina a motar Aimanah wacce yanzu tazama ta hawan Sumayya, Lina na kwance saman doguwar kujera da kumburarran goshi zuciyarta fal takaicin abinda Aimanah ta mata ga ba biyan bukata ga ciwo ga kuma ɓarnar datayiwa Sumayya na ruguza mata komai, ga bakin cikin shikenan ba ita ba zuwa taron gobe da zasuyi a kaduna to ina zata da wannan katon goshi, gabanta ne yafaɗi dataji sallamar Sumayya, tsaye kam Sumayya tayi a kanta tana aika mata banzan kallo "Kin kyauta akan wata bukata taki shine kika so ki ruguzamin rayuwa to ta Allah ba taki ba, yar akuya mai bin mata" dariya Lina tayi tana tashi zaune da kyar "Gara ma ni nice yar akuyar ba uwata ba tsohuwar najadu" "Lina ya isheki fa dani kike bada mahaifiyata ba ki tsaya a ni ɗin idan kika sake taɓo min mahaifiya inada makamin da sai na girgiɗe maki wannan auran wallahi" "Kin daɗe baki kashe min aure ba, anan anan ɗina kike" Lina tafaɗa tana nuna tafin hannunta "Ok haka kika ce to muzuba mu gani" Sumayya ta faɗa tana ficewa daga ɗakin, kai tsaye data fita wajan mai gadin gidan ta tsaya suka gaisa ta basa kuɗi masu yawa akan yabata lambar mai gidan, get man baiyi wani tunani ba ya bata lambar tasa a wayarta tai save ta fito ta shiga motar ta taja, kai tsaye gidan Feenah ta nufa a mutumce suka gaisa sun jima suna hira kana Sumayya ta faɗo kan zancan daya kawota, "Ni kuwa Feena ina vidio ɗin nan da kikaiwa su Lina itada malam randa mukaje ɗin nan?" Feena na dariya ta ce "Yana cikin wayata duk sanda naso nishaɗi kun nawa nake na kalla nayita dariya ni kaɗai" "Ki turo min ta whatsapp" "Ok bari na turo maki yanzu" ta kunna data ta tura mata, tana ganin ya shigo tai dariya bata jima sosai ba ta tafi. KANO Ammi gaba ɗaya hankalinta ya gama tashi da jin labarin da Shaheed ke bata kuka take sosai a cikin hospital ɗin, Momy da Yaya Ahmad ke lallashinta "Naso na gano wani abu sanda naje Abuja amma danayiwa Alhaji magana sai yace ba haka wai na cika zargi daga nan nabar maganar, kaico kaico da wannan auran na Aimanah tabbas gobe saina je abuja sai Mustapha ya saki yarinyar nan, hmmm Mustapha Allah ya.." "A'a Ammi dan Allah karki yiwa ɗan uwana baki" "Ko kusa Ahamad bazan taɓa aibata ɗan wani ba bare ɗana dana ɗauki cikinsa tsawon wata tara na shayar da shi na watanni goma sha tara ba baki zan masa ba Allah ya shirye sa zance" Aslam da Tasnim Momy ce ta wuce gida da su binciken likitoci ya tabbatar lafiyarsu kalau, Islam ce dai maleria da typod suka ci karfinta, saiko olsa data kamata hakan yasa aka ɗorata kan magunguna da allurai amma sun kwantar da ita a hospital ɗin danci gaba da kwaje kwaje, Alhaji Kamal ma yaji haushi da bakin cikin abinda yafaru hakan yasa yaɗau alwashin kafarsa kafar Ammi gobe da shi za'ayi tafiyar nan zuwa Abuja, AMARYA Shiri suke sosai na tafiya taron da zasuyi a kaduna Hanne an kasa zaune an kasa tsaya kasancewarta babba a harkar shiyasa take ta amsa kiran waya kala kala, wajan tara na safe suka ɗauki hanyar kaduna a motoci uku Hanne da Amarya da Rahila sai wasu matan guda biyu sune a sahun farko, driver ɗin Hanne ke jan motar tasu, kaguwa da Hanne tayi ta ganta a kaduna yasa ta azalzali driver ɗin dayayi gudu sosai suna gafda shiga zariya sukai mummunan hatsari ba kyan gani Hanne tuni ta amsa kiran Allah sakamakon kanta da babbar mota ta taka yai kaca kaca akan kwalta, Amarya kuwa a sume akayi hospital da su itada sauran yan motar, abin Allah driver ɗin ba abinda yasame sa sai buguwa da yayi a gefan kansa mota kuwa tuni ta tashi a aiki, Amarya lokacin data farfaɗo ta dawo hayyacinta shuru tayi tana kallon yan asibitin ba inda ke mata ciwo amma tayi tayi ta tashi ta kasa hakan yasa ta ɗaga hannunta ta kira wani likita dake tsaye kusada gadon wata mara lafiya da alama duba ta yake, sai da yagama da ita kana ya karaso inda Amarya ke kwance kan gado "Sannu kin farka kenan, ya kike jin jikin?" "Ba inda ke min ciwo sai dai nakasa ta shi zaune" zaro idanu likitan yayi alamar firgici ya ɗauko allura ya caka a kafarta yaga ko motsi batayi ba "Bakiji zafi ba" "Ba zafi, ji nake kafar kamar ba'a jikina take ba" "Hajiya ina yan uwanki, sai an maki hoton baya muga ya lakar ki take da alama fa kinsamu tsinkewar laka, hoton zai nuna mana in wanda zai gyaru ne sai ayi gyara" hawaye Amarya ta soma musamman bayan tafiyar likitan da driver ɗin su ya shigo shi yake shaida mata mutuwar Hanne da halin da sauran ke ciki, tayi kuka sosai tai nadamar wannan tafiyar tana faɗin data sani bata zo ba, shi ta bawa lambar Murja ya kirata ya gaya mata Mamanta tayi hatsari tana asibiti ana bukatar ganin wani nata, hankali tashe Murjana ta kira Sumayya ta gaya mata, ita kuma ta fara shirin tafiya zari'a itada Alhaji Jamil Ammi nayin sallar asuba bata koma barci ba ta hau shiri karfe shida na safe suka ɗauki hanyar Abuja itada Alhaji Kamal da Ahmad saiko driver ɗinsu, wajan sha ɗaya da wani abun na safiya suka shiga abuja gaban Ammi bugawa yayi sanda driver ɗinsu ya faka motar a cikin gidan Mustapha, jiki sanyaye Ammi itada Ahmad suka jera zuwa ciki musty na zaune saman kujera yayinda Sumayya ke tsaye tana danna waya murmushi shimfiɗe a fuskarta kamar ba ita Murja ta kira tana gaya mata mahaifiyarsu na hospital ba, ɗagowa tayi ta kalli su Ammi da suka shigo da sallama, daga kallo ɗaya bata sake yi masu wani kallon ba ta maida kallonta ga madubin wayarta tana cigaba da murmushinta "Ammi barka da safiya kune da safan nan, Ahmad bisimillah zauna" Mustapha yafaɗa yana nunawa Ahmad kusa da inda yake zaune, "Bazama mukazo yi ba, Mustapha ina Aimanah?" "Aimanah ai bata gidan nan Ammi tun jiya na sallameta na bata takarda ko Honey" yafaɗa yana kallon Sumayya "A'A kaga ba ruwana, karka sako ni a zancan ku yanzu matar nan ta ce na maka asiri ka rabu da matarka, bayan ni banma san anyi ba" "Ke!!! shiga hankalinki kisan da wacce kike magana" Ahmad yafaɗa a zafafe harda mikewa daga inda yake zaune yana huci kamar zai kai mata duka, Ammi kasa magana tayi sai ma buɗe ɗakin Aimanah da tayi ta shiga, shuru ɗakin sai darduma a shimfiɗe, takardar dake ajje saman gado ta ɗauka hannunta na karkarwa ta buɗe ta karanta _Ni Mustapha Kamal Sareena na saki Aimanah saki ɗaya_ dafa bango Ammi tayi tana hailala da tasbihi ga ubangiji lalle mutum abin tsoro futowa tayi daga ɗakin tana kalllon Ahmad, "Muje Ahmad" bata tsaya ba tayi gaba abinta, Alhaji Kamal na tsaye jikin mota yaga futowar Ammi da Ahmad harma da Mustapha da Sumayya, har kasa Sumayya ta tsugunna ta gaida Abba daya amsa fuskarsa ba yabo ba fallasa "Abba wai dama Aimanah bataje gida ba, tun jiya da yamma fa tabar gidan nan Mustapha ne ya bata takarda sabida ya kamata ta satar masa kuɗi, ba yanda banyi da ita ba akan ta zauna mu basa hakuri ta kafe sai da ta tafi ko ina taje, Allah yasa tana lafiya" Sumayya ta faɗa harda kukanta kamar gaske, kallon mamaki Ammi kewa Sumayya lalle mace shu'uma ce "Assha Mustapha garin yaya haka ta faru banyi farin ciki da jin maganar nan ba" "Abba ba wannan ba, bar waɗannan mutanan mu fara kiran yan uwa ko Aimanah taje kano" kusan duk wanda Ammi ta kira amsa ɗaya ce bata zo ba, haka ya kuma tasar hankalin Ammi sosai, hankali tashe suka baro Abuja suka juyo zuwa kano, Ammi kuka sosai take da tunanin inda zasuga Aimanah anan kano bincike sosai akayi har mutuware sai da Ammi da Ahmad suka rinka zuwa suna dubawa wai ko ta taho sukai hatsari ta mutu, wasa wasa tun ana ɓoye magana har magana ta fito sarari Aimanah ta ɓata, hanakali tashe yayu da iyayan Aimanah suka duro kano, Mus'af kamar yayi hauka lokacin da labari yaje masa yana sauka a nageria Abuja daman ya sauka sawa yayi yan sanda suka kama Sumayya da Mustapha da zargin sun ɓatar da yarinya, anan sell na yan sanda yabarsu ya hau jirgi ya wuce kano, sai da Sumayya da Mustapha suka kwana biyu a cell sannan Mus'af yafaɗa yasha faɗa a wajan Daddy shiya tilas ta sa aka sake su suka koma gida Sumayya na daɗa cin alwashi...✍🏻 [2/13, 4:46 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi Na Talatin da biyar* Hajiya Zainab zaune gaban gadon da Aimanah ke shimfiɗe kamar gawa, Muhd na gefanta yana dannan waya yayinda Azinatu ke zaune itama kan gadon daga gefan Aimanah, gaba ɗaya sunyi shuru abin duniya duk ya dami Hajiya Zainab zuciyarta fal da zulumin kar yarinyar nan ta mutu "Moha a fara binciken daga ina yarinyar nan ta fito, na tabbata zuwa yanzu iyayanta na cikin tashin hankali yau kwana shida fa kenan" "Mom wannan fa daga gani irin yaran nan ne dake aiki a gidajan masu kuɗi kilama sata tayi aka koreta daga inda take aikin" Azinatu ta faɗa tana hararar Aimanah wacce bata san tanayi ba "Wannan ce tai maki kama da masu aiki, ke dai kawai kin saba saikin ai bata mutum, ke bazaki canza hali bako, bar asibitin nan ki sani ɗan adam ba abin wulakantawa bane kilama tafi ki gata" Azinatu hararar yayan nata tayi tareda kyauda kai gefe "Moha bana son hayaniyar nan taku kuje gida dan Allah" "Gaskiyya Mom anemo wacce zata kula da yarinyar nan ki koma gida yaufa kusan sati kenan rabonki da gida, ga ranar Anty Ramla inda tana nan da tini ita ke kula da yarinyar nan" Muhd kallon Azinatu yayi ya fice daga ɗakin batare daya ce mata komai ba, da sauri ta mike tabi bayan Muhd tasan ba karamin aikinsa bane ya tafi ya barta anan, Hajiya Zainab mikewa tayi ta shiga bathroom tayi alwala ta tada sallah nan cikin ɗakin, tana zaune saman dadduma tai nafila raka'a biyu ta soma jero addu'o'i har barci ya ɗauke tana nan saman daddumar SUMAYYA Suna komawa gida daga stesion wanka kawai tayi ko magana da Mustapha batayi ba tai shirin tafiya enugu, gaba ɗaya ma ta manta da wata amarya dake kwance a asibiti ba lafiya, ta isa enugu lafiya ta zube gaban malam har kuka saida ta masa akan yataimaka mata kar asirinta ya tonu, wasu ɗalasimai yafara karantawa take wata tukunya ta bayyana a gabansa yacewa Sumayya leka kiga kanta tai kasa da shi tana leka cikin tukunyar Aimanah ce ta bayyana cikin tukunyar kwance kan gadon asibiti "Mu muka sakata wannan dogon barcin muna jiran kizo muji mai kike so a mata" "Malam amata duk abinda yadace nidai so nake Mustapha yazama nawa ni kaɗai" "Hhhhhjj shikenan zamuyi, zamu tashe ta daga dogon barcin da take aljani zai shafe tunaninta bazata iya tuna ita wace ba sai nan da wata uku sannan ta zama ba matar mijinki ba zata dawo hankalinta,muddin tana hankalinta asirin jikin Mustapha zai karye, Mijinki kuma mun rigada mun gama komai a kansa kije sai yanda kikayi da shi yanda kika dama haka zai sha ko kara kika ajje kika ce karya tsallaka bazai tsallaka ba" "Yawwa malam nagode," "Ba'a mana godiya kije, wannan tukunyar zansa aljani yanzu ya ɗauke ku keda tukunyar ya maida ku gida ki ajjeta waje mai kyau inhar ta sake fashewa to bani da abinda zan maki kuma ki kula sosai sannan in kina son magana da ni ki leka tukunyar nan ki kirani zan bayyana, rufe idonki" da sauri Sumayya ta rufe idanunta jikinta na karkarwar tsoro, tsawon lokaci idanunta na a rufe can taji kamar wacce aka ajje kan wani abu ta buɗe idonta tana buɗewa taganta zauna kan gadonta, zabura tayi har tana buge Mustapha dake barcin safe MURJA Kuka sosai take sanda taga Mama kwance a gadon asibiti ko zama bata iya yi, Alhaji Jameel shi yayi komai aka mata hoto wanda ya nuna lakarta ta rigada ta tsinke ba ita ba sake iya zama sai dai kwanciya, Amarya tayi kuka tai nadamar abinda ta aikata da bin son zuciyarta da tayi, Alhaji Jamil yadamu sosai ya rinka tambayar Dr ɗin ba yanda za'ayi ko zama a samu tarinka yi suka ce basuda kwarewa a wannan harkar sai dai zasu turasu kano asibitin kashi dake dala, a motar asibitin aka kawo Amarya asibitin kashi anan kano, bayan hotunan da sukai mata suka ce zasu mata aikin da zata iya zama amma itada sake taka kasa har abada, sanda aka gayawa Murja kuɗin aikin hankalinta yatashi naira miliyan huɗu da rabi, Alhaji Jamil shiya biya kuɗin yai komai aka mata aiki, alhamdulillah aiki yayi kyau sosai tana iya zama amma sai an taimaka mata sai dai bata iya tashi da kanta komai a inda take zaune take hakan yasa aka saka mata ledar fitsari, sanda aka sallamesu rasa inda zasuyi da Amarya Murja tayi, Amarya ma kuka tayi sosai na nadama yau sai gashi ta tina da iyayanta dake katsina can Murja da Amarya suka tafi a motar da Alhaji Jamil yasamo masu a tasha ya biya kwana ɗaya yabawa Murja ta dawo sabida jibi zasuyi tafiya, Dakyar da lallashi iyayan Amarya suka karɓeta dan har rantsuwa sai da Babanta yayi baza ta zauna masa a gida ba sai da Murja ta nemo wani wan baban yayi masa magana kana aka bata ɗakin da zata zauna, Murja ta kira Sumayya tana kuka ta gaya mata halin da mama ke ciki, hankalin Sumayya yatashi hakan yasa tabi jirgi zuwa Katsinan itada Murja suka shiga suka fita suka samo wata tsohuwa da za'ana biyanta zata kula da Maman tasu dan mahaifiyarta rantsuwa tayi da abinda zai kasheta bazata taɓa Amarya ba, washe gari Murja da Sumayya suka baro katsina, kafin wani lokaci Amarya baya ya rarake yayi wani zurfi sai wari da yake fitarwa ko ɗakin ba kowa ke iya shiga ba duk da kuwa tsohuwar na matukar kula da Maman, Sumayya ita ta koma aka samu nurse ɗin dake zuwa tana wanke wajan kullum, daya warke kuka sai wasu tsutsotsi yan mitsi mitsi da suke futowa daga gabanta cukus ba kyan gani Amarya ta rame ta kanjame duk da kuwa su Murja na matukar kula da ita suna ajje mata komai na amfani AIMANA Sai da tai sati guda bata ko motsi sai yau data cika sati guda sannan ta buɗe idanunta, lokacin Mom na ɗakin da sauri ta mike ta kira Dr ta cikin telephone ɗin dake cikin ɗakin nan da nan sai ga Dr da Nurse a tare, Dr yakarasa gaban gadon da Aimanah ke kwance wacce keta dube dube "Sannu yaya jikin?" "Da sauki ta faɗa a hankali" "Ya sunanki,kinsan wannan?" Dr ya tambayya yana nuna Hajiya Zainab "Ban san sunana ba, itama ban santa ba" "Yasalam" Nurse tace tana komawa gefe ta tsaya, Hajiya Zainab ta share hawaye tana zubawa Aimanah idanu "Hajiya abinda muke gudu yafaru fa sai dai zamu ɗorata akan magani mu gani" "Yanzu ina ne ke maki ciwo" "Bako ina" Aimanah ta faɗa a hankali "Hajiya zamu sallame ku ku koma gida sai dai zakuna zuwa ganin likita duk sati, sannan ayi kokari a samo yan uwanta ina zaton in taga wani nata komai nata zai dawo dai dai" "Insha Allah zamu bincika Dr" Hajiya Zainab ta kira Moha yazo ya ɗauke su, Aimanah da idanu kawai take binsu, sosai Mom ke kula da Aimanah gefe guda tana binciken yan uwan Aimanah, wasa wasa Aimanah sai da ta shafe watanni biyu da wani abu tana cikin wannan halin, Zaman Aimanah a gidan zama ne na gata sosai Mom da Muhd suke kula da ita, a wajan Azinatu kawai take samun damuwa, Aimanah shuru shuru ta koma bata cika son zama cikin mutane ba kusan ko yaushe tana ɗaki, cin abinci wanka sallah komai sai Mom tace tayi sannan take, yau gidan antashi sosai da murnar dawowar ɗan Hajiya zainab tun safe Ramla dake aure a kaduna tazo, sai ɗorawa da saukewa ake Hajiya Zainab haifaffiyar nan garin Abuja ce, mijinta tuni Allah ya masa rasuwa tana zaune gidanta itada yaranta guda huɗu Muhd shine babba sai Yasar Ramla sai auta Azinatu, Ramla an mata aure tuni tana kaduna tareda mijinta Allah bai basu haihuwa ba, Muhd baiyi aure ba andai saka masa rana da yar kanwar babansa, Yasar shekarunsa bakwai kenan rabonsa da nageria yana zaune a madina inda yayi karatu tuni harya fara lacture a jami'atul madina, takurawar da Mom ta masa na rashin zuwa gida yasa zai kawo ziyara ya koma, sai da suka gama komai suka gyara gidan yanata tashin kamshi sannan Muhd ya zo suka tafi airport ɗakko sa sabida jirgin da yasar ya biyo na gafda sauka, Ramla Azinatu su suka tafi ba yanda Mom batayi da Aimanah ba wacce suke kira da Aysha ba kan tabi su tace bazata ba hasalima komawa tayi ɗaki ta kwanta, Yasar rungume Muhd da Ramla yayi yana kissin ɗinsu ta ko ina "Nayi kewarku sosai, Yaya Moha ka kara girma, Anty Ramla tawa kin kara kiba" dariya duka sukayi banda Azinatu dake can gefe tana taɓe baki, dariya Yasar yayi sanda ya hangi Azinatu "Autar Mom sarkin rigima haka kika kara tsayi, amma dai taliya Mom ke baki ko" "Kaifa daman bakinka baya shuru, wuce muje" Moha yafaɗa yana rike da jakar kayan Yasar, tunda suka shiga mota bakin Yasar bai yi shuru ba sai surutu yake dan dama shi ba baya ba wajan magana, har suka karasa gida suna yi da Ramla Moha sam baya saka masu baki danshi mutum ne ba mai son magana ba, "Our wellcome ustaz" Mom tafaɗa sanda ta rungume Yasar, Sun batar ta kawai yake ta ko'ina yana rungume da ita "Mom nayi kewa" yafaɗa yana share hawaye "Nima nayi kewar surutun nan naka, ince dai larabawa basu canza min kai ba" "Ai wallahi ko kaɗan Mom ɗanki bai canza ba, tunda fa muka tawo yake surutu shida Ramla, surutu cai cai kamar yaci aku nifa harya samin ciwon kai, Dan Allah Mom kar a ce ya zauna a ɗakina kamar yanda muke da, ga ɗakin Ramla can ya sauka anan, bazan iya da surutun Yasar ba" "Caii wai nine mai surutun, Mom inama ɗakin Yah Moha ɗin yake tabbas can zan sauka yau kwanan hira zamuyi anjima ba'ayi hirar zumunchi ba" "Mom ina Aysha ne, banga motsinta ba" Moha yafaɗa yana kallon kofar ɗakin Mom "Tun bayan fitar ku ta kwanta barci, ke Azinatu taso ta, tazo aci abinci da ita" "Mom wace Aysha ko anyi bikin Yaya Moha ne banda labari" "Wata yarinya ce fa Mom ta kaɗe ta wata uku kenan amma an rasa iyayanta take zaune anan" Azinatu ta faɗa tana taɓe baki, hararta Anty Ramla tayi kana ta shiga ɗakin Mom inda Aimanah ke kwance "Anty Ramla kun dawo?" "Mundawo Ashanty Mom tace ki fito aci abinci ga Yasar ma yadawo" mikewa Aimanah tayi tana gyara zaman doguwar rigar dake jikinta tabi Ramla suka fito tare, da sauri Yasar ya kalli yarinyar da ta fito tareda Ramla zaro idanu yayi sanda idanunsu suka gauraya dana juna "Kambu, Mom maza bani ruwan zam zam a jakata" da sauri Aimanah ta juya zata koma ciki, caraf yayi ya ruko hannunta ya zaunar da ita nan saman tiles yana zare idanu, "Kai ɗago ka kalle ni," yafaɗa da karfi yana zare idanu, kai Aimanah ta fara ɗagawa, "Azinatu Ramla kubar falon nan" Yaseer yafaɗa cikin bada umarni "Wai Yasar ban gane ba mai kake wa yarinyar nan haka ne, maca ce fa kake kiranta da kai" "Zauna Mom da aljani kuke tare, asiri ne a jikin yarinyar nan bani zam zam dan Allah" Sim sim Azinatu tayi ta fice daga gidan gaba ɗaya jin an ambaci aljani, Anty Ramla zama tayi tai tagumi tana kallon Aysha dake bubbuga kafa "Bazaka ɗago ka kalle ni ka gaya min waya turoka ba" nan ma kai Aimanah ta kuma ɗagawa kanta na kasa "Anty bani cup" ta tashi ta ɗakko cup ɗin a kicin ta dawo ta basa, zam zam ɗin hannunsa ya fasa ya tsiyaye a cikin cup ɗin ahankali yafara karatu cikin ruwan, tsawon lokaci kana ya kalli Mom "Mom rike min cup ɗin nan ki rike sosai, zan matse bakinta ki zuba mata ki rage min kaɗan" Mom tayi yanda yace ɗin sauran daya rage ya cewa Ramla zoki shafa mata a jikinta, Ya soma karatun suratul bakara a hankali cikin kira'a mai daɗin sauraro "Wayyo wayyo ku daina zamu fita zamu fita, daman aiko mu akai turomu akai mu shiga jikinta mu ɗauke mata tunaninta ta manta komai har zuwa sanda zatayi idda ta zama ba matar Mustapha ba, yau kwana huɗu kenan data kammala daman muna shirin tafiya, kana kona mu kana konamu kabari zamu tafi" "Zaku tafi kamar ya ku zauna, ina mijin nata yana ina" "Yanzu haka yana wajan aikinsa" "Mai sukai maku da zaku rana auran sunna" "turomu akai kishiyarta ce ta turo mu" "To ku fita kuma ku karya asirin da kukai masu, kuna jina" "Munji zamuyi yanda kace" "Nafa sanku bakuda alkawari, in bakuyi abinda nace ba zansa a kawo min ku nan kuna ji" "Zamuyi komai yanzu ma" shuru Aimanah tayi tareda jero atishawa, can kuma ta buɗe idanunta ta mike a guje zata fita, rike ta yayi gam yana kallonta "Kinga nutsu kina cikin aminci" Wani kuka ta saki tareda kokarin kwace rukon da yayi mata "Musty ka sake ni barin gidan nan zanyi, kariga da ka yanke igiya ɗaya ta auranmu ka sake ni nasamu na fita daga wannan gidan na bala'i" "Kinga buɗe idanu ki kalle mu sosai nan ba gidan ki bane, Mom ta bike ki kusan wata uku kenan" da sauri ta buɗe idanunta tana kallonsu ɗaya bayan ɗaya "Ya sunanki" Moha ya tambaya a hankali "Aimanah Farouk mai naira ni haifaffiyar kano c.........nan ta basu labarin ta da abinda ya fito da ita daga gida, Mom sosai ta tausaya mata anan take Aimanah ta bada lambar Ammi aka kirata a waya, Ammi dan Murna ji take kamar ta fasa wayar ta shigo ciki, cewa ma tayi gatanan zata biyo jirgi tazo Abujan, Mom ta hana ta tace su yakamata suzo gobe zasu biyo jirgin safe, Yasar mikewa yayi ya shiga ɗakin Moha yayi wanka kana ya fito, kallon Aimanah yayi yana murmushi "Sannu Ummu ya kike ji, kanki baya ciwo ko" kai ta girgiza alama e "Ba da kai zaki min magana ba baki zaki buɗe kimin magana ɗago ki kalli idanuna naga wani abu" ɗagowa tayi tana kallonsa da fararan idanuwanta, wani abu yaji ya tokare masa a kirji, ya lumshe idanu yana ambaton Allah a hankali, yana buɗe idonsa sukai ido huɗu da Mom murmushi mom tayi tana bin Yasar ɗin da kallo yanda ya kafe Aimanah da idanu, kallo ɗaya inkayi masa fuskarsa zata fallasa asirin zuciyarsa....✍🏻 07039793439 [2/13, 4:46 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi Na Talatin da shida* "Kazo ka zauna kaci abinci sai kaje ka kwanta ka huta" Mom tafaɗa tana kallon Yasar daya kafe Aimanah da kallo,shafa kansa yayi kana yaja kujera ya zauna, "Ummu kinci abinci" Aimanah tayi murmushi batare data ce komai ba, Anty Ramla da Moha suka kalli juna suka fashe da dariya, Aimanah gaba ɗaya ta kasa sakewa idanun Yasar take ji a ko ina na jikinta, bata wani ci dayawa ba ta mike zuwa ɗaki "Ummu ki tsaya na baki habbatus sauda ki turara, sannan ki maida hankali sosai wajan yin azkhar na safiya da maraice ki yawaita karanta kur'ani kina kuma yawan saurara a wayarki" "Batada waya ai" Anty Ramla ta faɗa tana kallon Yasar "Bari inna fita anjima gaida gwaggo mariya zan taho mata da waya" "Da wuri haka" Moha yafaɗa yana dariya "Kasanmu a lamarinmu ba ɓoye ɓoye, sak muke tafiya ba kwana kwana" "Yanzu dai so kake kace kaga mata" "Ta aure ma insha Allah" ya maidawa Anty Ramla martanin maganarta "Tana dai da mijinta, kajira kaga yanda zata kaya" Mom tafaɗa tana kai lomar abinci bakinta "Mom tariga tayi idda fa, ba wata uku tai a gidan nan ba" "Hakane tayi idda yau kwana biyu kenan datai wanka, amma dai kabi a sannu karka zurma "Mom nafa riga na shiga irin sosai ɗin nan" yafaɗa yana dariya, Barci Yasar yayi na awanni sai yamma yatashi ya sake wanka ya fita ya zaga su gaisa da yan uwa, sai bayan sallar insha yadawo a hanyarsa ta dawo wa ya tsaya babban shagon sai da wayoyi ya saiwa Aimanah waya Infinix hot 50 pro, da sabon layin da yayi regester da kansa, lokacin daya dawo gaba ɗaya suna zauna a danning ana cin abincin dare "Mom shine ba'a jira ni ba" "Ina kuwa zamu jira ka Yasar, ka sani dai dokar Mom ce in lokacin cin abinci yayi ba a jiran wanda baya nan inya dawo ya ci shi kaɗai" "Ok naji, Ummu zubamin abinci kamar wanda zaki iya cinyewa" Dariya Aimanah tayi ta soma zuba masa abincin cikin sanyi jiki, "Yawwa barshi haka ina zan kai wannan abincin in da ina cinye kamar wannan aida tuni nafi haka kiba, Mom dafa sai dai a kara girman kofar shugowa" "Yasar ka barni naci abincina karna kware kai wai dole in kana waje sai kasa mutum dariya" "Mom nafison kullum na rinka ganin fuskarku wasai ba damuwa" Mom dai batace masa kanzil ba harta gama cin abin cinta tsawon mintina suna nan zaune a wajan, Aimanah ita ta fara mikewa zata bar wajan, Yasar ya jawo ledar daya ajje kasan kujera ya mikewa Aimanah "Ummu ga wayarki kamar yanda na faɗa maki, ki buɗe ta ki saita komai zamuyi waya cikin dare" hannu Aimanah tasa ta karɓa tareda masa godiya,mikewa Mom tayi "Mom gashi" "Na gani Aimanah Allah yasa albarka" "Ya Moh kaga yabani waya a tayani godiya" "Dai dai Allah yasanya alkhairi "Anty Ramla kinga" Aimanah ta faɗa tana mika mata ledar, Antyn ce ta zaro wayar daga kwalinta ta buɗe ita tasa mata screen gard ɗin da wayar tazo da shi, tasa sim ta kunna wayar kana tace taje ta sata a caji, Aimanah ta karɓa ta juya zata bar wajan Azinatu taja tsaki tareda bangaje ta tabar wajan, Aimanah murmushi tayi kawai ta wuce ɗakin Mom, Aimanah cikin barci taji wayar na kara, cikin magagi ta ɗaga kiran "Ummu bakiyi barci ba" taji muryar Yasar ta doki kun nan ta, cikin magagin barci ta ce "Barcin fa nake" dariya sosai Yasar yayi "A barcin kike magana kenan? wastsake dan magana zamuyi dake ta fahimta" "Yasar barci nake ji sosai mubar maganar sai da safe" "Bazan iya ba Ummu, Kaunarki ta shige ni sosai tsoro nake kar nayi jinkiri wani ya rigani samun fili a zuciyarki" "Filin zuciyata babu kowa a ciki Yasar sa Yasar, ba yanzu ba banan kusaba bance bazan kuma bawa wani fili a zuciyata ba amma dai ba yanzu ba" ɗif ta katse kiran tareda saka wayar a jirgi ta maida kai ta kwanta, Ahankali ta furta "MUSTY" share hawaye tayu tareda runtse idanunta hawaye naci gaba da fita, Yasar naushin fulon daya ke kai yayi da karfi yana faɗin "Ya Allah" haɗe da sakin numfashi, Moha gyara kwanciya yayi tareda buga tsaki "Ka takuramin fa Yasar kazo kana waya murya kasa kasa kamar munafiki, yanzu kuma ka fara kai naushi," filon sa ya ɗauka ya sauka daga gadon ya koma saman doguwar kujera yasa fulon ya kwanta yana mita "Gara nayi nesa da kai kafin ka kai min duka" Yasar dariya kawai yayi baice komai ba shima ya mike ya shiga bathroom ya ɗauro alwala yazo ya tada sallar nafila, bayan ya gama jero nafilfili daya saba yi duk dare yai addu'a, sannan ya mike ya sake kawo wata raka'a biyun yai addu'ar istikhara na neman zaɓin Allah" yasake addu'o'i ya kalli agogo yaga huɗu da kwata hakan yasa ya fita zuwa masallaci, can ya zauna yana karatun kur'ani har akayi sallar asuba yadawo gida shida Moha wanda yabisa masallacin bayan anyi kiran sallar asuba, yana ganin Muhd ya shiga ɗakin Mom su gaisa shi kuma ya wuce zai kwanta yana cewa Moha "Agaida min Mom sai nayi barcin safe zan zo mu gaisa kafin ku wuce kano" "Ai dama ka zo kun gaisa ɗin a mota zamu tafi karfe bakwai zamu fita kaga sai kayi barcin sosai" juyowa Yasar yayi suka shiga ɗakin tareda Muhd, Mom na bathroom Aimanah na zaune saman dadduma tana azkhair, sallamar da sukayi ta amsa ta ɗago kai ta kallesu "Yaya Moha barka da safiya anta shi lafiya" "Lafiya kalau Aysha ya kika tashi" "Aysha kuma yaya Aimanah dai, wannan babban sunane sunan mamata" "Ummu ina kwana tunda ni baza'a gaida ni ba" Yasar yafaɗa yana zama ɗan nesa da ita kaɗan, "Ni na isa na ki gaida yayana, barka da tashi ya gajiyar hanya" "Gajiya tabi lafiya Ummu," yaɗan matsa kusa da ita ka ɗan yana magana kasa kasa yayin da kan Aimanah ke cikin kafafuwanta fuskarta ɗauke da murmushi har Mom ta fito daga bayi kallo ɗaya taiwa Yasar ɗin ta fita daga ɗakin tana jin tausayin ɗan nata yanda so yai masa mummunan kamu, a kicin ta tarar da Anty Ramla nata kokarin haɗa abin kari dan ganin sun fita da wuri "Sannu Ramla, Allah ya maki albarka yabaki yaran da zasu faranta maki fiye da yanda kike min Ramla" "Amin Mom" Ramla ta faɗa tana murmushi, kafin bakwai sun gama shiryawa zaman break kawai akai shima a gurguje akai dan ganin an fita da wuri, Ramla ta fito da jakar kayan Aimanah suka fita compound inda Moha ke cikin mota yana jiran fitowarsu, ahankali yake takowa har zuwa inda su Aimanah ke tsaye itada Mom "Mom yanzu da ban fito ba tafiya zakuyi" Mom mota ta shiga bakinta ɗauke da addu'ar abin hawa bata tankawa Yasar ba, "Ummu dan Allah ki rike min alkawari insha Allah gobe zan zo kano muyi magana ta gaske" "Sai kazo amma zaka iya auran bazawara mai ƴaƴa uku" zaro idanu Yasar yayi yana kallon Aimanah cikeda mamaki "Wai dan Allah da gaske, nayi farin ciki daya kasance munada yara zan aureki a haka zan kuma haɗa da yaranmu na rike ina maku fatan sauka lafiya" "MOM Allah ya tsare hanya" yafaɗa sanda ya leka kansa cikin motar" "Yasar kana ɓata mana lokaci fa, ance kazo a tafi da kai kace ba yau ba amma ka tsare mu da zance" "Lafafa min Ya Moha a sauka lafiya" yafaɗa yana rufe murfin motar yaja baya yana kallon Moha yaja motar suka fita daga gidan, gwauron numfashi yaja ya jima nan tsaye a wajan kana ya koma ciki ya koma barci, Tafiyar awanni biyar da wani abu yakawo su Aimanah garin kano ita ke nunawa Moha hanya bayan sun shigo kano har suka karasa gidansu dake gadon kaya, SUMAYYA Murmushi take ta dokawa sanda Dr ya basu sakamako tanada ciki na wata huɗu wanda ita batayi zato ko tsammani ba "Mustapha kaga kyautar da Allah ya mana" Musty baice komai ba, saima kallo dayabi Sumayya da shi ita da Dr suka gama maganganunsu suka taho gida bakin Sumayya yaki rufuwa sabifa murna, suna shiga gida Sumayya taga Lina da feenah a zaune cikin falon, turus tayi taja ta tsaya bakin kofa kamar bazata shigo ba sai kuma dai ta shigo ciki tana binsu da kallo "Lafiya naganku yanzu ba sanarwa zaku zo" "Da in zamu zo sanarwa muke ai, Sumayya abinda kika yi kinyi adalci kenan ki ce na tura maki vidio ashe ke da manufa kikai haka, to burinki ya cika mijin Lina yamata saki uku yanda ya saketa ya rabata da yaranta wallahi kema yau sai mijinki ya sake ki kila ma ke har sai an haɗa maki da duka, yau zamu nuna maki mu yan asalin hau ne, sai kinga hau yau yasin" Feenah ta faɗa tanayin gaba zuwa ɗakin Sumayya, Lina tabi bayanta da sauri Sumayya ma ta rufa masu baya, Kayan ɗakin suka fara watsi da shi harda kayan sawarta, Sumayya ta shako wuyan Lina ta shake duk yanda Feenah taso ta kwaceta ta kasa hakan yasa ta janyo karfan labule ta bugawa Sumayya zafin azabar daya ziyarci idanunta yasa ta hankaɗa Feenah tayi baya sai gata ta faɗa kan tukunyar tsafin Sumayya, wani bakin hayaki ne yatashi ya dunkule waje ɗaya yai sama ya saki kara da rugugi kamar na hadari, Feena da Lina da gudu suka fice daga ɗakin dayake futar da tiriri "Wayyo Allah na shiga uku ni Sumayya shikenan asiri ya tonu shikenan komai ya karye wayyo ni rayuwata, Feenah kun cuce ni nayi dana sanin saninku a rayuwata kun ruguza min komai" ta zube kan gwiwoyinta tana fashewa da kuka Mustapha kamar wanda aka tasa daga barci haka ya mike firgigit daga kan gadon dayake kwance ya fito yana sake tina mummunan mafarki da yayi, tun da yafito daga ɗaki yake kwaɗawa Aimanah kira "Reina! Aimahh!! Aimah!!! wai ina kika shiga ne, Aslam Tasnim Islam Gwaggo Fulani ku fito mana dan Allah kuna ji ina kwaɗa maku kira" turus yaja ya tsaya lokacin daya buɗe kofar ɗakin Aimanah da yayi kura sosai alamar anjima ba'a amfani da ɗakin, da hanzari ya karasa ɗakin yara ya buɗe nan ma kamar na Aimanah ya haɗa uwar kura harma tafi ta ɗakin Aimanah, hankalinsa ne ya kuma tashi tuna mafarkin da yayi na wulakancin daya rinka yiwa Aimanah da yaranta bama abinda yafi ɗaga masa hankali kamar wai a mafarkin da yayi wai ya saki Aimanah" hankaɗa kofar ɗakin Sumayya yayi ya shiga, Sumayya idanunsa kawai ta kalla tagano tabbas asirinta fa ya riga ya tonu hakan yasa ta fara ja da baya ta haɗa hannuwa waje ɗaya alamar roko "Dan Allah kayi hakuri Mustapha son zuciya ne da bin ruɗin kawaye yasa na aikata komai, na tuba na bika bazan sake yin asiri ba dan Allah kaje ka dawo da Aimanah zamu zauna lafiya ba faɗa ba gaba wallahi ni zan rinka mata komai zan zama kamar baiwarta nidai fatana kawai ka zauna dani" dafe kansa yayi da yaji yana matukar sara masa ya rike kan da hannunsa yana ambaton Allah "Wai Sumy mai kike faɗa haka, kina nufin ba mafarki nayi ba, abubuwan da duk nagani a zahiri ne da gaske na saki Aimah na saki reina wai" Mustapha yafaɗa hankali tashe yana matsowa kusa da Sumayya yayinda ita kuma take yin baya harta dangana da bango "Ka gafarce ni Mustapha aikin asiri ne" wata shaka Mustapha ya kaiwa wuyan Sumayya yana ihu da faɗin "No wallahi no kar ya ne ni na saki Aimanah ina bazaiyu ba" shake wuyan yayi kamar zai kasheta idanunta suka firfito waje "Sumayya na sake ki na sake ki na sake ki saki uku" yafaɗa yana yin wurgi da ita ta faɗa gefe tai suman wucin gadi, a guje kamar ta ɓaɓɓe ya fita daga ɗakin yaje ya ɗau wayarsa ya na dannawa Ammi kira AIMANA Tsabar kagauta da ɗokin ganin ahalinta da gudu ta fita daga motar ko gama tsayawa motar ɗ batayi ba, da gudu Ammi wacce ke gidan tun safe ta fito tazo ta rungume Aimanah suka fashe da kuka tare "Sannu Aimanah sannu munyi kewarki munyi kuka na rashin ganinki da tunanin halinda kike ciki" "Saudah wai maye haka kamar wata karamar yarinya kin wani rungumeta kuna kuka" Mah tafaɗa sanda ta fito compound ɗin "Barni nayi kuka Yaya Aysha baki san yanda naji ba barni na koka zuciyata ta sami salama" Mah amsar baki tayi ta masu jagora zuwa ciki kasancewar lokacin sallah yayi ko zama basuyi ba akai alwala Moha yabi Ma'aruf zuwa masallaci matan kuma sukai sallah nan cikin gidan ɗakin Mah, sai da akai sallah sannan kuma aka shiga gaisawa duk a zaton Mom Ammi itace mahaifiyar Aimanah shiyasa kusan ita tarinka bawa hakuri kan abinda yafaru, Ammi wayarta ce tayi kara alamar kira na shigowa sai da gabanta yafaɗi ganin Mustapha ne ke kira, tayi mamaki matuka dan rabon data ga kira irin haka tana tunanin tun kan rabuwarsa da Aimanah hakan yasa ta fita daga falon "Hello Ammi ki yafemin dan Allah ina Matata da yarana" "Masha Allah, Allah abin godiya Mustapha kaine da gaske" "Ammi da gaske nine ina matata da yarana" "Aimanah gata nan cikin gida yanzu suka zo daga abuja yara kuma suna school sai shida na yamma Shaheed zaije ya ɗakko su" "Ammi kano zan tawo nariga da na datse duka igiyoyin aure na da Sumayya na mata saki uku kafin nazo nan nasan ke ba ganin girman zunubin nan data aikata zakiyi ba, da zuciyarki ta musulumci saiki ce na barta da tun abaya kin barni na sahale mata da duk haka bata faru ba" "Assha Mustapha saki irin haka ba daɗi fa banso kayi uku lokaci guda ba" "Ammi bazan iya sake zama da mishirika ba, gaba inaga kashe ni zatayi" "Allah ya kyauta Mustapha, yanzu dai muna tareda baki zan koma ciki sai kazo" sallama sukayi Musty ya koma ɗakin Sumayya da har sannan take tsugunne kan kafafunta tana kuka, jawota yayi har compound ya watsota waje ya maida kofa ya rufe, mikewa Sumayya tayi Allah yasa da mayafi a jikinta har jakarta na kafaɗarta futa tayi ta tai tafiya mai nisa sannan ta sami inda tasai takalmi kai tsaye tashar mota ta nufa ta hau motar zuwa katsina, cikin motar kuka take sosai tana daɗa cin alwashin duk yanda zatayi sai ta koma gidan Mustapha ko zatayi yawo tsirara Abbas zaune a falo fuskarsa cunkushe da damuwa tsawon watanni a haka yake, Rumana ta kasa gane kansa ita dai zata iya cewa tun bayan ɓatan Aimanah Abbas ya koma haka duk iya kokarinta nason ganin ta goge masa wannan damuwar data bayyana karara a fuskarsa ta kasa, wayar Rumana dake ajje kusa da shi ce tayi kara ya kalli sreen na wayar ganin Ammi ke kira ya mikewa Rumana wayar ya mike zai bar wajan ihun murnar da yaji tayi yasa shi juyowa a fusace zai mata faɗan abinda tayi, tsallan data yi ta rungumesa ya hana shi magana "Honey Yaya Aimanah yau ta dawo gida Allah alhamdulillah" wata nauyayyar ajjiyar zuciya yayi wacce tasa har Rumana sai da ta kalllesa kallo irin na tuhuma, fuskarsa ta kalla take taga ba wannan kuncin sai wani zallar farin ciki da ya mamaye fuskarsa "Abbas daman wannan damuwar danake gani a fuskarka tsawon lokaci duk akan ɓatan Aimanah ne, kana nufin har yanzu akwai son Aimanah a ranka ashe farin ciki kayi da Yayanmu ya sake ta" a razane Abbas yaɗago yana kallon Rumana da tsawon rayuwar auransu bata taɓa kiran zallar sunan sa ba sai yau "Rumy maine haka kuma ni muka..." "Kimin shuru bakada abinda zaka faɗa min" Rumana da gudu ta faɗa ɗaki Abbas ya rufa mata baya yana kiran sunanta....✍🏻 [2/13, 4:46 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi Na Talatin da bakwai* "Rumy maiye haka dan Allah ki tsaya ki fahimce ni mana, wallahi bako ɗigon son Aimanah a zuciyata ina jinta kamar yar uwata wacce muka fito ciki ɗaya, wani ɓangaran kuma ina mata kallon yayar matata" "Haka zakace min mana zaka min daɗin baki, inka ɓoye sirrin zuciyarka ai fuskarka ta fallasa asirin zuciyar" kusa da Rumanan ya karasa ya jawota jikinsa yana shinshinar wuyanta "Ba wata mace a wannan xuciyar ta Abbas saike Rumy, kece dai ke kaɗai zaki mulkin wannan zuciyar yanzu ko gaba har zuwa karshan rayuwata Abbas bashida wata mace bayanke bazance na maki alkawarin bazan maki kishiya sabida komai mukaddari ne amma dai ina da tabbacin bazan iya son wata macan bayan ke ba, kece komai nawa" Sosai kalaman Abbas sukai tasiri a xuciyar Rumana anan dai suka raya sunna daga rigima aka ɓige da soyewa, tare sukai wanka yana shirin fita tace "Yaushe to zanje kanon" dafe kansa yayi yana kallon cikin idanunta "Ke dai kam Maman twince kin fiye rigima yanzu dai so kike mu kara wani faɗan, ko inaga dai so kike mu koma scound round" yafaɗa yana kashe mata ido ɗaya "Nidai ba daɗin bakin da zaka min wallahi sai naje kano naga Yaya Aimanah kuma tare zamuje da kai" zaro idanu yayi tareda haɗe fuska "Ke dan Allah yaushe rabon da ki ganni a kano inaga tun randa aka ɗaura mana aure da ke, bana jin nan kusa zan iya zuwa kano" yafaɗa yana lumshe idanu tareda kwantar da kansa a fuskar gado, alamun damuwa suka bayyana karara a fuskarsa, Rumana kallon mijin nata tayi tana murmishi tareda kudurce wani abu a ranta hakan yasa ta zauna kusa da shi tasa hanunta cikin nasa tana mirzawa a hankali tsawon lokaci suna a haka kafin tayi magana "A wannan karon fa sai kaje kano, mai kake tsoro a kanon badai karka fama mikin son Amanah bane to itama tana kano kuma a yanzu kanada damar da zaka mallaki Aimanah, Abbas nabaka dama idan har Yaya Aimanah ta amince da kai ka aure ta" buɗe idanu Abbas yayi yana kallon Rumana daya soma tinanin ko kishi yaɗan taɓa mata kai ne, "Ke!!! Rumana dawo hankalinki please" "Ahankali na nake Abbas da gaske har cikin zuciyata gaskiyya nake faɗa maka inma bazaka iya yakin ba ni zan zama sarkin yakin neman auran Aimanah gimbiyar Abbas" Rumanah tafaɗa tana dariya "Rumana abin nan bamai yiyuwa bane ki bar faɗa dan Allah, Aimanah fa yayarki ce" "Dan tana yayata aiba haramun bane addini bai halatta haka ba" "Amma al'adarmu ma bata aminta da hakan ba" "To addini ko al'ada wanne ka zaɓa" "Mubar maganar nan please tana samin ciwon kai, ki shirya zamubi jirgi zuwa kano, amma hotal zamu sauka" "Ni bazan kwana hotal ba kamar wata.."Dan Allah bana son musu a wannan yana yin kiji abinda nace kawai" batace masa komai ba tabisa da kallon tausayi har ya fice daga ɗakin MUSTAPHA Jirgin karfe huɗu na yamma Mustapha yabi zuwa kano, Ahmad yaiwa waya suka haɗu a airport na kanon shiya ɗakko sa zuwa gida acikin mota suna tafe ba wanda kewa wani magana can dai Mustapha da shirun Ahmad ya damesa ya ɗago ya kallesa suka haɗa idanu, Ahmad kauda idanunsa yayi yana kallon kwalta batare daya ce komai ba "Duk haushi na kuke ji ko?" Mustapha ya tambayi Ahmad yana kallon sa, Ahmad dake tuki da hannun daman shi yayinda ɗayan hannun ke tallafe da kansa batare da ya kalli inda Mustapha yake ba yayi kamar baiji abinda ya ce ba can dai yamaida masa da "Rayuwarka ce fa Yayanmu kayi duk yanda kaga dama kawai dai inajin haushin ka ne daka saki Aimanah inda ace iyayanmu basuda fahimta mai kake tunanin zai faru da tuni zumunchi ya ɓaci" "Na rantse da Allah Ahmad ban saki Aimanah ba, hauka nayi da zan rabu da farin cikina" wani kallo Ahmad yaiwa Mustapha kafin ya furta "Ga takarda nan raɗau da rubutunka ai baza'a maka karya ba" "Ahmad inma na saki Aimanah ai ba da sani na nayi ba, kariga da kasan komai kasan asiri gaskiyya ne ni kaina yau dana dawo mutum nai mamakin abinda naiwa Aimanah ganin abin nayi kamar a mafarki ni ban san ma da wanne ido zan kalli Mah da Aimanah ba" "Da idanun da kake ganin kowa ka azabtar da yaran nan baka ga Mamana Islam yanda ta koma ba, olsa typoid maleria duk ita kaɗai Allah ne yayi tanada nisan kwana Allah yakai Shaheed gidan yatawo da su watanta guda a hospital sannan ta warware har yanzu batada wata cikakkiyar lafiya olsa tariga da ta taɓa mata zuciya" zaro idanu Mustapha yayi yana kallon Ahmad, "Ahmad kaini school ɗin su naganta dan Allah wayyo ni kaico" "Shaheed yatafi ɗakko su mu karasa gidan kawai" shuru motar tayi ba wanda ya kuma magana har suka karasa gidan, sun tarar Ammi ta dawo faɗa sosai taiwa Mustapha kan abinda yafaru ta nuna masa mihimmancin addu'a da azkhair taku ce lalle ya je har gida ya bawa Mah da Daddy hakuri, harya mike zai futa zuwa gidansa sai kuma ya koma ya zauna yana kallon Ammi idanunsa suka kawo hawaye "Ammi ya aure na da Aimanah?" "Aure ya rigada ya mutu Mustapha, Aimanah yanzu ta zama ba matarka ba, ban kuma lamince ka koma mata ba ka barta ta sami wani ta aura kaima ka nemi wata Mustapha yara dai Allah ya raya zan rike su a waje na" "Ammi shikenan na hakura da Aimanah, Ammi zuciya ta bazata iya jure wannan hukuncin naki ba" "Nariga na zartar da hukunci bakai ba Aimanah bazaka ɓata mana zumunci ba nida yayata muzo muna jin haushin juna, auran zumunchi ma an daina sa a family gaba ɗaya kowa ya nemo a waje" tana gama faɗar haka ta mike tabar wajan, Mustapha damuwa kunci gaba ɗaya suka mamaye zuciyarsa ya wuce gidansa ya buɗe ɗakin Aimanah ya kwanta ya saki wani kuka mai sauti, kirjinsa yaji ya masa nauyi shikenan shikenan shida Aimanah har abada yanaji yana gani zata auri wani ba shi ba "No wallahi bazai yuwu ba, zuciyata bazata ɗauka ba, wayyo Aimanah Rayuwata Farin cikina Kaunata" ya jima nan kwance shuru yakasa taɓuka komai. SUMAYYA Sosai take kuka a mota har suka karasa katsina Allah yasa da kuɗi a jakarta harma da ATM card ɗinta duka a ciki, sosai hankalinta ya kuma tashi dataga halin da Amarya ke ciki ta rame tai baki sosai daga ka shiga gidan kasancewar ɗakinta ne farko inka shigo zaka fara jiyo wari da ɗoyin da take, matar dake kula da Amarya daman ta gaji neman hanyar barin aikin take tana ganin Sumayya tazo ta gudu aka bar Sumayya da aikin kashi da fitsarin Amarya idan tana gyarata haka zata toshe bakinta da face mask inta gama tayita kwara amai dama ga cikin jikinta kafin wani lokaci itama Sumayyan ta kwanta ciwon laulayi, Murjana na zaune lafiya itada Alhajinta da yara uku na Kishiyarta da har yau basu san inda take ba, yaran daman ba wani sabawa sukai da Mamansu ba tun suna tambayat tana ina har suka ma daina suka maida Murjana komai nasu itama ta rungume su suka zama tamkar ita ta haifesu, har sannan suna tareda nanny ɗinsu sai kanwar mahaifiyar Alhaji Jamil ɗin da suka ɗakko daga kebbi take nan tare da su, duk inda Alhaji Jamil za shi suna tare a nan gida ko a kasar waje, ko kusa batayi saken da zata basa wata dama da zai kula wata mace ba, yau tana kwance a ɗaki barci harya fara ɗaukarta da gudu Ansar ya shigo ɗakin yana tsalle irin nasu na yara "Momy kizo ga mamanmu tazo tace ki fito" gaban Murjana sai da ya buga kamar bazata fito ba sabida batasan da mai tazo ba sai kuma dai ta kamo hannun Ansar suka fito tare, jefa idanunta ko ina take a kayataccan falon nata tana hangen inda zata ga Maman Jannart muryar Rahila taji daga bayanta "Sannu Murja sannu da kokarin kula da yara" da sauri Murjana ta zauna nan kasan tiles tana kallon matar da taji muryat Rahila daga bakinta idanu buɗe take kallon gurguwar matar da toyayyar fuska "Wai ina Maman Jannart ne?" Murjana ta faɗa tana kallon su Inna Fure da Nanny ɗinsu Jannart "Kema baki gane ni ba Murjana, kaico nayi nadama da biyewa gangar sheɗan na taka rawa, Murjana a daran da Alhaji jamil ya sake ni gidan hajiyar nan naje na kwana washe gari muka tafi Kaduna tare da sauran wasu matan mukai hatsari Hanne ta mutu sauran na motar ma sun mutu daga ni sai wata muka rage ita lakarta ta tsinke ni kuma na karye fuskata ta kone Allah yataimake ni ban rasa gani na ba sai kafata ɗaya da aka yanke sabida rashin kulawa ba kuɗin gyaran karayar da nayi kuɗin da aka min aiki ma aka cire kafar sai tallafi asibitin suka nema min da kyar na samu, da aka sallame ni rasa inda zani nayi sai kauyanmu na koma can na samu ɗaki na zauna nake fita bara ina samun kuɗi dana tara su ne na shigo mota yau na zo na ganki na baki amanar yarana na shaida maki nabar maki su duniya da lahira, nasan ni tawa ta kare mutuwa zan ina rokon ki kiyafe min in Abban jannart yadawo kice ya yafe min," ta karasa faɗa cikin kuka, Murjana itama kukan take sosai kenan dai tafiyar Rahila ɗaya da mamansu kaico rayuwa bata masu daɗi ba, sun jima anan falon anata kuka har Rahila ta mike zata tafi, Murjana kuɗi ta bata masu yawan gaske tace mata tasai waya in tana bukatar wani abu ta kirata ko bata zo inda take ba zata saka driver ya kawo mata, Rahila ta kalli Ansar da ya lankwaɓe a jikin Murjana tana murmushi ta ce "Zo nan Ansari na muyi sallama" sake shigewa jikin Murjana yayi yana kankame ta alamar bazaije wajanta ba, "Murja ki rike min yaran nan da amana dan Allah ki kula da tarbiyarsu da kawayan da zasuyi mu'amala kawa sharrinta nada yawa ita taja ni ta kaini ga halin da nake ciki, Allah yamaku albarka yarana" tafaɗa tana share hawaye, Jannart ta rungume maman tasu tanata kuka dakyar aka rabata da mamanta AIMANA Bayan sunyi sallah aka ci abinci, Ammi tuni ta wuce gida tace yara na hanyar dawowa daga makaranta, Mah da Mom hira suke sha sosai kamar daman sun san juna, Yaya Muhd na tareda Ma'aruf da Azinatu suna zagaya gari suna ganin garin kano Azinatu zuwanta na farko kenan garin da taji ya matukar burgeta har tana sha'awar zama a ciki, yan awannin da sukai tareda Ma'aruf ta kamu da matsananciyar kaunarsa, Aimanah ko na tare da Anty Ramla a ɗakin Aimanan na yammatanci suna ta hira, har Mistapha ya zo gidan yatafi basu sani ba, yanata leken inda zai ga Aimanah amma bai ga motsinta ba da kunya kuma ya tambayi Mah ina Aimanah, Mus'af daya koma Rasha yau dai sunyi waya da Aimanah yafi sau goma lokaci bayan lokaci yake kiranta yana jin muryarya, bayan mangariba suna nan falo anata hira sai ga Rumana, da gudu Aimanah taje suka rungume juna suka saki kuka lokaci ɗaya, Mah na dariya ta ce "Wai to kukan na me ne kuke yi?" ke Aimanah sake ta baki ga halin da take ciki ba, da sauri Aimanah ta kalli Rumana ta rike baki tana dariya kasa kasa "Ikon Allah himma bata ga rago sannu maman twince, hala wasu twince ɗin kika samo mana" turo baki gaba Rumana tayi ta baje kasan carfet tana maida numfashi, Abbas ne ya shigo yana rike da twince da sauri Mah ta mike ta amshi yaran tana dariya "Sannu Abbas keta bari da rukon yara, bisimillah zauna" Mah tafaɗa tana nuna masa kujera, har kasa ya tsugunna ya gaida su Mah da Mom kana ya zauna inda Mah ta nuna masa ya zauna "Ya Abbas barka da dare ya hanya ya twince da mamansu" Aimanah ta faɗa batare data kalli inda yake ba tasa hannu ta ɗauki usaina tana mata wasa "Masha Allah Rumana mai kike basu haka tubarkallah masha Allah ɓulɓul da su" Aimanah ta faɗa tana ɗaga Usaina sama, Abbas kasa kasa yake jifan Aimanah da wani sassanyan kallo, Rumana na ankare da shi ko kaɗan bataji komai a ranta ba, ita ganau ce ba jiyau ba akan kaunar da Abbas ke wa Aimanah bata wasa bace tasa ni koda yace mata ba Aimanah a zuciyarsa faɗa kawai yayi tasan baikai har zuciyarsa ba YASAR [2/13, 4:46 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹 Story and writting by Mamie Yusuf Daboo🥰 ☀️ *First Class Writer Asso*☀️ Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation *Shafi Na Talatin da Takwas* Yinin Ranar jinsa yayi sakaka gaba ɗaya bayada wani kuzari tunanin Aimanah gaba ɗaya ya cika masa zuciya addu'a yake Allah ya mallaka masa ita, washe gari jirgin karfe shida na safe yabi zuwa kano, hotal ya kama ya zauna yaɗan warware gajiya yai barci wajan goman safiya yatashi yai shiri cikin dakakkiyar shadda blue ɗinkin ta zarce ya kafa hula zanna bukar yai matukar kyau bakin takalmi yasa mai matukar kyau wanda suka matukar dacewa da shaddar dake jikinsa, fitowa yayi wajan hotal ɗin yana tsayawa mota ta faka a gabansa "Yasar Mahmud Ahmad" wanda ke tuka motar yafaɗa, kai kurum Yasar ya gyaɗa alamar e ya shiga motar da driver ɗin ya buɗe masa mirfin motar ya zauna nan kusada mai tuka motar, ahankali da nutsuwa driver ɗin ke bin location har suka karasa gidan su Aimanah, yana sauka a kofar gidan ya kira wayar Aimanah mintina kaɗan ta fito inda yake tsaye yana murmushi "Barka da zuwa kano ya Ustaz" Aimanah tafaɗa tana kallon Yasar da ke tsaye kikam yana binta da kallo, Nesa da su kaɗan Abbas ya faka motar sa ya kifa kansa saman sitiyarin motar yana sakin numfashi da sauri sauri, ɗagowa ya kuma yi yana kallon Aimanah da wani daban ta zage sai dariya take masa, da mugun gudu yatashi motar yai ribas yabar layin batare da yayi abinda yakawo sa ba, Aimanah jerawa sukai zuwa ciki itada Yasar suna magana, har ciki suka shiga tare gaisawa sukai da Mah cikin girmamawa Hanne ta kawo masa ruwa da lemu ta gaidasa ta fita, Azinatu ta fito daga ɗaki tana murnar ganin Yasar, kama baki Yasar yayi cikeda mamaki "Baku tafi ba daman, ai na zaci kun ɗau hanya" "Bamu tafi ba, Mah ta hanamu tafiya sai gobe mu tsaya mu gaisa da Daddyn su Aimanah yau zai dawo daga saudiya" gyaɗa kai yayi kana ya ce "Ina mom ɗin to?" "Sun fita itada Ya Muhd da Ma'aruf" shuru Yasar yayi har sanda Aimanah ta ajje masa plate ɗin dake shaƙe da kayan snack "Jazakallahu khair" Yasar yafaɗa yana kallon fuskar Aimanah, murmushi Aimanah tayi ta zauna kujera dake kallon wacce yake kai, Samosa ɗaya ya ɗauka yai bisimillah yakai bakinsa, lumshe idanu yayi sakamakon wani musulmin daɗi daya ji daga samosan buɗe idanunsa yayi kan Aimanah "Masha Allah Samosan nan yayi daɗi sosai, idan munyi aure kullum shi zakina bani ina ci haɗeda shayi a birnin madina" dariya Aimanah da Azinatu sukayi a lokaci ɗaya, Yasar kuwa sake ware idanuwa yayi yana kallonsu yanda suke dariya "Wai da nayi magana mai nace ne naga kuna dariya haka" dariyar suka kuma yi Azinatu harda rike ciki tana gangarowa daga saman kujera zuwa kasan carfet "Yaya Aimanah Allah kisawa Yaya Yasar waigi karfa ya faɗi" Yasar bai sake bin takansu ba har sai da yaji ya koshi, kana ya kalli Aimanah "Kurratu ain kuna da leda na saka sauran snack ɗin nan na tafi da su" "Kai Yaya Yasar karfa kayi abin kunya a gidan surukai" "Au haka ne fa, Azinatu bari na kama kaina" Aimanah murmushi kawai take tana kallon Yasar wanda shima ita yake kallon, ganin kallon da suke yasa Azinatu ta mike ta basu waje su zanta "Ina yarana" Yasar ya tambayi Aimanah "Nima tunda nazo ban saka su a idanuna ba" Aimanah ta basa amsa cikin yanayin damuwa, har sannan kallonta yake yana nazarta fuskarta "Ba'a nan garin babansu yake ba, ko suna can wajansa a Abuja" "Suna nan garin wajan Ammi," "Ammi ba ita bace mamanki" "Kakar yaran ce, kanwar Mamana" numfashi Yasar ya fesar kana ya kwantar da kansa saman kujera bayan wani lokaci ya ɗago yana kallon Aimanah wacce ke wasa da zoban dake hannunta "Wai kina nufin auran zumunchi kuka yi da tsohon mijin naki" kai Aimanah ta gyaɗa masa "Wayyo ni" Yasar yafaɗa yana sake maida kansa saman kujera, Rumana ce ta fito daga ɗakin Mah kunnanta kange da waya da alama waya take da Abbas, dai dai sanda ta karaso inda suke ta katse kiran, kallon Yasar tayi ta kuma maida kallonta ga Aimanah ta taɓe baki ta juya zata koma inda ta fito "Kizo ku gaisa Rumana, Yasar ne yanzu yazo daga Abuja" "Ina kwana" Rumana ta faɗa daga inda take taci gaba da tafiya batare da ta jira cewar sa ba "Kanwarki ce? muryarku iri ɗaya haka ma tafiyarku" "E! kanwata ce" Aimanah ta basa amsa Da gudu yaran suka shigo suna kwaɗa kiran "Amma, Amma" mikewa tsaye Aimanah tayi fuskarta shimfiɗe da Murmishi ta buɗe hannayanta suka shiga ta rungume su tana sumbatarsu "Aslam Tasnim ina Islam" "Tana tareda Abie yanzu zasu shigo ya tsaye kulle mota ne", Aslam yabata amsa, Tasnim bai yi magana ba sai kara riketa da yake yana sauke ajjiyar zuciya, "Tasnim baka canza ba, kana nan da shurunka" "Amma ina kika tafi kika barmu, muyita kuka Ammi tace school kika je sai kin daɗe zaki dawo" Aslam ya tambayi Aimanah, kafin ta basa amsa ta ga shigowar Mustapha hannunsa rike da Islam dake tafiya a hankali, gaban Aimanah ya buga lokacin da idaninta suka shiga cikin na Mustapha, Musty daya kafe ta da idanunsa tunda ya shigo harya karaso inda take, Islam da gudu ta faɗa kan Aimanah tana faɗin "Amma daman da gaske Ammi take zaki dawo, Amma karki kuma tafiya ki barmu muna sonki ko Aslam" Islam ta faɗa tana kallon Aslam da baice komai ba yana jikin Aimana da jikinta ya ɗauki rawa musamman da Mustapha ya zauna a kujerar da ta ke kai,tana jiyo sanda suke gaisawa da Yasar "Aimah tunda bazaki gaida ni ba ni bari na gaida ki ina kwana" kasa magana tayi sai ma mikewa da tayi zata bar wajan, hannunta ya riko cikin hannunsa ta tsaya cak, a zafafe ta ce "Yayanmu shika min hannu" "Bazan shika ba, inace hannun matata na rike" "Matarka a ina na zama matarka ada ne zaka iya kirana da wannan sunan na amsa ba yanzu ba daka datse igiyar auranmu guda ɗaya" "Aimah dan Allah dan Allah ki tsaya muyi magana ta fahimta" "Bakada wannan sauran lokacin a wajena Mustapha, babu sauran wasu kalamai da suka rage da zaka iya gaya min ka barni, ka fita a rayuwata dan Allah" ta faɗa cikin Kuka, mikewa yayi daga zaunan da yake yai taku biyu zuwa inda take ya tsaya a gabanta har sannan hannunta na cikin nasa "Ɗago idanu ki kalle ni Aimanah, kisa idonki cikin nawa ki gaya min bana sonka Mustapha ni kuma na maki alkawarin daga ranar bazaki sake ganin mai kama dani ba, zan nesance ki nisan da bazamu kuma haɗuwa ba har abada" hannunta ta fisfe daga cikin nasa da gudu ta shige ɗakinta ta kwanta kan gado tana kuka sosai, yaran bayanta suka biyo ganin tana kuka suka fito suka shiga ɗakin Mah SUMAYYA Gaba ɗaya rayuwar duniyarta ta gigita gidan ba daɗi ƴan kuɗin account ɗinta duka ta cinye su wajan siyan abinci, Murjana ta kira ta roki ta taimaka mata da dubu goma zata zo kano, tana ganin alart ɗin ta saka hijab ta nufi tasha ta hau motar kano, kafin su sauka a kano amanta yafi biyar gaba ɗaya ta galabaita sai tsangwamarta yan motar suke, a wahale ta shiga gidan Ammi kai tsaye sashin Ammin ta nufa, Ammi na magana da Shaheed sai ga Sumayya kamar wacce aka jefo "Ammi dan Allah ataimaka min da abinci" tafaɗa a wahale sanda ta zauna kasan carfet, Ammi kamar bazata bata ba sai kuma ta mike ta kawo mata abincin harda ruwa da lemu, Shaheed sai hararta yake kamar ya kai mata duka haka yakeji, duk yawan abincin da Ammi ta kawo mata sai da ta cinye sa tas sannan ta gaida Ammi cikin kuka take bata hakuri akam ta taimaka tasa Mustapha ya ɓ Maidata wallahi ta tuba bazata sake halinta ba "Sumayya yace fa saki Uku ya maki ta ina zai maidaki ki dai yi hakuri Allah ya haɗa kowa da rabonsa na alkhairi," "Ammi dan Allah karki ce haka, kodan abinda yake cikina a tausayamin" zabura Shaheed yayi kamar zai kai mata duka har sai da Ammi ta rike sa "Shegiya muna fuka makaryaciya a ina kike da ckin inma cikin ne dake to bana yayanmu bane can kije ki nemi ubansa" "Na rantse da Allah ba cikin wani bane wallahi na Mustapha ne ban taɓa sanin wani ba inba Mustapha ba" Sumayya ta faɗa cikin kuka, Ammi wayarta ta ɗauka ta kira Mustapha wanda ke zaune a gidan sa yana tunana yanda sukayi da Aimanah yaga kiran Ammi kamar bazai ɗaga ba ya mike zai fita zuwa gidan sai kuma dai ya ɗaga kiran "Zo maza Mustapha" bata jira abinda zai ce ba ta katse kiran da sauri ya fita zuwa gidan, zuciyarsa har zullo tayi ganin Sumayya zaune a falon Ammi "Ammi mai wannan mushirikar take yi a gidan nan" "Zauna Mustapha magana zamuyi" a hannun kujera ya zauna yana kumbura fuska "Mustapha wai Sumayya nada ciki kasani" "Na sani Ammi taje ta haifa tana haihuwa ta kawo min abin data haifa bazan taɓa barin jini na a wajanta ba, da da dama ma wallahi cikin zubar da shi za'a yi," murmushi Ammi tayi tana kallon Sumayya cikin tausayawa "Sannu! yanzu ina maman taki?" "Mama batada lafiya ta sami matsalar laka tana katsina" "Shikenan to Allah yabata lafiya, yanzu ki koma gidanku na nan baya ki share ɗakin ki ki zauna" "Ammi ya..." Ammi ta katse Mustapha da faɗin "Yimin shuru Mustapha, ka ɗakko duk wani abu da kasan nakane kabar mata gidan ta zauna tana ɗauke da cikinki har yanzu nauyinta na kanka har zuwa sanda zata haihu ta yaye ɗan" "Ammi bazan taɓa barin jini na a wajan Wannan bakar kadarar ba, tana haihuwa zata bani ɗana ko nononta bana bukatar ya sha bare ya gado wasu muna nan halinta" Sumayya dai mikewa tayi tana yiwa Ammi godiya tanan cikin gidan tabi kofar da zata sadata da gidan nasu, juyi tayi tai tsalle ta kwanta kan kujera ganin burinta nason komawa Mustapha yafara cika, lambar malam ta kira sai dai taki shiga jiki san yaye ta shiga ɗakinta ta faɗa gado tai kwanciyarta ba sallah bare salati daman tuni ta daɗe da jingine sallah a babin rayuwarta, Ammi tasa Mustapha yaturawa Sumayya dubu ɗari a account ɗinta danta rinka samun abu mai kyau tana ci, Mustapha rai ɓace ya dawo cikin gidan nasa yaɗau duk wani abu daya san nasa ne ya maida sa ɗakin Ahmad acan yagama week end ɗinsa safiyar Litinin yabi jirgin safe ya koma Abuja, sanda ya koma gida sai yaji gidan yai masa faɗi shi kaɗai ba motsin kowa, ko ina ya kalla sai moment ɗinsu da Aimanah ke faɗo masa rayuwar da suke tare itada yara da yanda yake shiga cikinsu suyita tsalle tsalle wani bin harda tsairan gudu, hawayan fuskarsa ya share yana jin zuciyarsa ba daɗi, ba shiri yabar gidan ya nufi wajan aikinsa, Sumayya tana ganin alart ɗin dubu ɗari daga Mustapha har rawa ta taka tana cewa gobe sai enugu wajan malam, sai dai safiyar litinin ɗin Ammi tazo har gida tasata a gaba sukaje asibiti duk wasu abu daya dace ayiwa mai ciki shi aka mata sannan aka bata ranar dazata dawo awo, safiyar talata kuwa Sumayya sassafe tabi mota zuwa enugu, sai dai tayi rashin sa'a ta tarar bukkar Malam a kone kurmus a wajan wasu take jin labarin ai kawai gani akayi bukkar ta kama da wuta ta kone malam ɗinma a kone aka fito da shi wuta duk ta gama kone sa a haka aka bunnesa, ko kaɗan bataji zuciyarta ta yi laushi ba saima cin alwashi datayi zata nemi wani malamin daga zarar ta koma kano. Aimanah rayuwarta take ta jin daɗi da walwala tuni ta koma B U K ta ɗora da karatunta, ta koma gidan redion data ke aiki da taci gaba da aiki da su, yara na hannunta shi yasa hankali kwance take rayuwarta har kiba tayi ta kara haske, Yasar ya matsawa rayuwarta duk da ya koma Madina amma kullum yana nacin kira akan ta amince da soyayyarsa ta taimaki rayuwarsa a ɗaura masu aure ta biyosa madina su zauna, ita sam yanzu aure baya gabanta karatu da aikinta kawai tasa a gaba, koda zatayi aure ma batajin zata auri saurayi bare Yasar data ke ma kallon da kaɗan ya girme ta a yanda take zato yasar bazai wuce sa'an Ma'aruf ɗin gidansu ba, har Ɗanbatta taje ta ɗakko Gwaggo Fulani suka ci gaba da zama tare tana kula da yara, Mah na Saudiyya wajan mijinta Tuni suka koma har Ma'aruf da ya kamu da soyayyar Azinatu harma manya sun shiga an tsaida masu ranar biki, shiyasa Yasar yake ta mata nacin ta Amince sai ayi bikin tare danasu Yaya Ma'aruf ɗin, Mustapha tunda ya koma Abuja bai dawo kano ba sai da ya shafe watanni biyu sai dai suyi waya da Ammi yaransa ma yasa an kawo masu waya sabuwa dal a kwali Gwaggo Fulani ke haɗasu da yaran su ɓata lokaci suna hira, Aimanah na kallonsu wani lokacin har vidio call zata ga anayi, Musty yasha kiran wayar Aimanah bata ɗagawa sai dai kullum kamar shan maganin bature sai ya mata tex messages sau uku a rana duk da bata taɓa masa reply ba bai fasa ba, Maza da dama na zuwa wajan Aimanah masu santa da aure amma ko kaɗan bata taɓa bawa wani dama ba, wani Alhaji Sadam ne ma takan ɗanyi waya da su kusan kullum shi tana ganin mutumchi da kimar sa yaransa biyu mata maman yaran ta rasu shekaru biyu kenan bai kara aure ba acewarsa yana neman wacce zata iya kula masa da yara bai samu ba sai da yaga Aimanah yaji a ransa itace wacce yake fata da burin ta zama matarsa yana ganin zata kula masa da yaran sa, ya mata alkawarin da zarar ya aure ta ta tawo da yaranta zai haɗa duka ya rike su.....✍🏻