Compiled By Umar Dalha Funtua. All thanks to Allah S.W.T for giving me the chance, priviledge and ability to write this Novel, i dedicate this first page to my sweet siblings and our Mum like no other, Allah ya bar min ku Ameeen. My Special greeting goes to my frnd my abokin fada *Captain Ajay* ⚓ Allah ya kare ka ya biya maka bukatun ka na alkhairi a duk inda kake. 💫 *Noorul Huda* 💫 1...... A hankali ta karashe rufe windows din dakin ta juya tana kallon makeken agogon dake manne bango dakin, karasawa gefen gado tayi ta xauna murya can kasa tace "Rain? Not today pls..." Bude kofar dakin aka yi ta juya da sauri Mahaifiyarta dake tsaye bakin kofar tace "Ki tabbatar kin sa sweatern ki, kiyi addu'a ki kwanta haka kuma sai da safe!" Bata ce komai ba uwar ta juya ta fita, sake kallon agogo tayi taga bakwae da kusan rabi, Wayarta dake ajiye kan gado ya shiga ring ta mike ta dauka ganin me kiran ta daga ta kai kunne tace "Hello!" Daga daya bangaren aka ce "Kar ki ce min baxa ki xo ba sbda ruwa?" Ajiyar xuciya ta sauke tace "Kema kin san mumy...." Katse ta tayi tace "A'a gaskiya baki min adalci ba, it's already dark just sneak out ki fito yanxu bbu wanda xai sani ae kince Abba baya gari fahhh" D'an langwabar da kai tayi tace "Alryt bari inyi kokarin yin hakan, gani tahowa" daga haka ta ajiye wayar, cikin kankanin lokaci ta gama shirinta ta dau jakarta ta saka waya da kudi snn ta dau rain coat ta saka, ta kashe fitilar dakin, cikin sanda ta fito daga dakinta, ta dinga bin corridor da kallo dim haske ta hango daga bedroom din Mum dinta ta sauke ajiyar xuciya a hankali don tasan me take yi, tana gamawa kuma xata kwanta sai kuma gobe, da sauri ta sauka downstairs taga duk an kashe fitilun parlon ta nufi kitchen tana lalube lalube ta bi ta kofar kitchen din ta fita ta tura a hankali ba tare da ta rufe ba, ko da ta isa gate mai gadi bai ce mata komai ba ta bude gate ta fita, da sauri take tafiya don anguwar tsit bbu kowa sai haske, a haka ta isa babban titi ta samu d'an sahu ta fadi masa inda xata ta shiga, haka kawai gabanta ke faduwa don tunda take bata taba abinda ta yi ba yanxu, gashi dai yau kawa ta sa ta, kawar ma warce basu jima da sanin juna ba, basu kuma wani saba ba, takwas saura ta isa wani babban gidan duk da ruwan da ake tsulawa hakan baxai hanaka jin sautin kidan dake tashi a gidan ba, ta shiga gate jiki a sanyaye ta karasa kofar da xai kai ta babban parlon da ake birthday din, mata ne da maxa a cakude ana ta rawa abun ba tsari, k'awartata wato celebrant din ta hango ta ta karaso da sauri cikin flowing gown dinta ta rungumeta tace "Ohh babe am happy you came to ki cire rain coat din mana, you are already missing" sauke hulan tayi tace "But i never knew the birthday will be like dis, it's just disorganized...." Katse ta tayi tace "Nothing is disorganized a nn idan xaki karaso ayi bidiri da ke ki karaso" tabe baki tayi ta cire rigar ruwan jikinta, doguwar gown na kanti ne jikinta me kyau ta saki dogon gashin kanta kawarta ta kashe mata ido tace "Waow besty kinyi kyau ina ma Boo dinki ya gan ki yanxu" murmushi tayi tace "Uhm" hannunta ta ja suka karasa inda ake ta shagalin birthday din, waje ta samu ta xauna ta dau maltina ta bude tana sha tana kallon yanda mata da maza ke ta watsewar su ga hayaki ko ta ina, duk bata saki jiki ba a gun abun ka da wanda bai saba ba, a xuciyarta kuwa tunani ta dinga yi anya xata iya ci gaba da tarayya da Clara kuwa, she's rough, bata yi minti goma da xama ba wani guy ya dawo inda take ya xauna yace "Hi babe how you doing?" Ta d'an kallesa tace "Good" yace "Pls may I know you futher?" Girgixa kai tayi tace "Noo" yafito ta da Clara ke yi yasa ta mike ta nufeta, ya bi ta da kallo, can ya kalli drink din da take sha, cikin seconds din da basu wuce 7 ba ya fiddo wasu kwayoyi ya jefa a gwangwanin malt din snn ya fiddo wayarsa da sauri yana dannawa, ba a dau lkci ba ta dawo ta xauna ta ajiye sticks din meat dake hannunta da cake ta dau gwangwanin malt din ta ci gaba da sha, ya cije lebe yana d'an murmushi bai ce mata ba ita ma bata ce masa ba, bayan kusan minti goma taji ta fara jin bacci sosai, mikewa tayi da kyar tace "Excuse me" ya mike shi ma yace "Ohh no probs, gida xa ki ne?" Ta d'an kallesa sai kuma tace "Ehh" yace "Toh mu je kiyi ma kawar ki sallama sai inyi dropping din ki that's my duty here" bata ce masa komai ba suka karasa gun Clara, da mamaki tace "Haba babe da wuri haka" a takaice tace "Ehh am feeling sleepy" kallon guy din tayi sai kuma tayi murmushi tace "Toh shknn take her home directly plss Sam" Yace "Alryt" da sauri ta nufi kofa jin kamar kanta na juya mata, suna fita ya kama hannunta suka nufi gun motarsa, xuwa lkcn ruwan ya d'an tsagaita sai yayyafi, ya bude gaba ya sa ta snn ya shiga ya ja motar suka fita, basu yi nisa ba yyi parking yace "Baby ina ne gidan naku" ta kallesa da sexy eyez dinta tace "Tarauni...." Ya kamo hannunta yace "Ohh that's very farrr" bata ce komai ba ya fara shafa hannun a hankali yana jan long fingers dinta, ta lumshe ido tace "Take me home...." Jawota yyi jikinsa yana shafa fuskarta lkci daya ya shiga tura hannunsa rigar ta ya kwantar da kujeran motar cikin tsawa tace "Stop itt...." Sosai idonsa ya kada cikin lallami yace "baby...." Wani mari ta sauke masa ta bude motar ta fice ya xaro ido hannunsa dafe a kuncinsa, fitowa yyi da sauri shi ma tana ganin haka tafara gudu duk da juya mata da kanta yake, iya karfinta take gudun yana biye da ita, suka yi nisa sosai, taji ta kasa ci gaba da gudun, a gaban wani gida ta hango wani mutum tsaye yyi backing flowers waya na kare a kunnensa, tana haki ta karasa kusa da shi jikinta na rawa tace "Help plsss...." Tsit tayi ganin taban dake dayan hannunsa ta juya da sauri xata bar wajen ya yarda taban ya fincikota, ihu ta fasa dai dai lkcn da Sam ya karaso gun, kallo daya biyu yyi ma mutumin sai kuma ya juya ya koma inda ya baro motarsa, sai ta gwammace da ma a hannun sam din take akan wnn mutum kkrin kwace hannunta take ko ina na jikinta na rawa amma ta kasa, wani kallo yake mata daga sama har kasa da manyan idonsa, ta fashe da kuka a tsorace tace "Don Allah kayi hakuri ka kyaleni" fixgota yyi dai dai fuskarsa yace "Me ya fito da ke da?" Turarensa mai dadin kamshi da ya hade da warin taba duk ya isheta, ganin jiran amsa yake bakinta na rawa tace "Birthday din k'awata na fito" daga sama har kasa yake kallonta yace "Shine aka biyo ki xa ayi maki fyade knn?" Hawaye ne ya shiga bin kuncinta ta kasa cewa komai yace "Da na san daga inda kika fito knn da na bari yayi fata fata da rayuwar ki...." Daga haka ya tura ta ta bar gun da sauri tana gudu, bin ta yyi da kallo har ta kusan shan kwana sai ya ga ta tsaya, wasu samari biyu ya hango tsaye gabanta duk da ba wani haske gun, ta juya xata canxa direction wani ya sha gabanta, jan ta yaga suna yi xuwa gun wani mota da alama tasu ce ya xaro ido kafin ya ankare har sun isa gun motar yana kuma iya jiyo ihunta daga inda yake duk da uban nisan wajen, wani mahaukacin gudu ya saka kamar xai tashi sama kafin yaje har sun tada motar sun ja, yace "Shit!" juyawa yayi ya koma gun motarsa da sauri ya shige ya kwasa a dari da sittin ya bi bayansu, da kyar ya kamosu a dai dai wani round about ya kusa cin karo da su ya bude motar ya fito daya daga samarin ma ya fito da shirin masa bala'in ya buge masa mota bai ko sauraresa ba ya bude backseat din motar yaga bakinta suka rufe da wani kyalle, fixgota yyi daga motar duk suka tsaya kmr sokaye suna kallonsa ya bude tasa motarsa ya jefata a baya ya koma driver seat ya shiga ya ja motar, tafiya yayi me nisa kafin yayi parking gefen titi ya juya yana kallonta kife kanta ya ga tayi a bayan motar, yace "Keeeh" ya ji shiru, wani tsawan ya sake mata nn ma bata dago ba, ya bude motar ya fito da sauri ya bude backseat din ya dago kanta yaga ta dawo, xaro ido yayi ya shiga motar da sauri ya rufe ya dago kanta, komawa baya yyi jin warin abinda ya bugesa, yayi saurin cire kyallen ya wurgar waje, gashin kanta ya mayar baya yana kallon fuskarta, idonta a lumshe ga lashes kamar an dasa su ne, hancinta dogo kamar an xana mata, a hankali ya sauke idonsa kan karamin bakinta me kala biyu pink nd black, dauke kansa yayi sai kuma ya kwantar da ita ya bude motar ya fita ya rufe ya jingina jikin motar yana tunanin yanda xai yi da ita, d'an bude ido yayi sai kuma ya bude motar da sauri ya shiga ya dagota ya kai hannunsa dai dai hancinta, tsaki yayi ya saketa ya dafe kansa, can ya kwanto a hankali ya kai bakinsa dai dai nata, ya sa hannu ya bude bakin nata ya daura nasa kai ya shiga hura mata iska, ya kusa minti bakwae yana haka tayi wani uban atishawa ya dagata ya koma baya da sauri ya ciro handki aljihunsa yana goge bakinsa da fuska, a hankali ta bude ido sai kuma ta mike xaune ta rike kanta, shi dai kallonta kawae yake, sauka yaga take son yi daga kan kujera ya rike ta yace "ke malama stay still...." Ta fashe da kuka tana jujjuya kanta tace "Where is this please take me home my head is aching" wani uban harara yayi mata kamar tana kallonsa yace "Wani ya fito da ke yawon birthday?" Da kyar ta bude idonta da yayi jajur tana kallonsa muryarta na rawa tace "Take me home pls kaina na ciwo...." Tsaki yaja ya jefar da handki din hannunsa ya fito ya koma front seat ya tada motar ya hau titi, a fusace yace "Ina ne gidan naku?" Cikin muryar kuka ta gaya masa, waka ya kure yana bi don ma ya daina jin sautin kukan nata, parking yyi kamar wanda aka umarta yyi hakan, sai kuma ya fara reverse har ya iso wani babban pharmacy da ya wuce, ya bude motar ya fito ya shiga ciki bude motar tayi xata fita ta kasa don ji tayi kmr duniyar aka aza mata a kai ga wani jiri da take gani, ta fashe da kuka ta koma ta xauna, ba a dau lkci ba ya dawo rike da ledan Magani ya bude inda take ya jefar mata snn ya shiga maxaunin driver ya tada motar suka bar wajen, tana masa kwatance har suka iso gidansu, ya juya yana kallonta da d'an mamaki bayan ya gama kare ma makeken gidan kallo, ta bude motar da kyar xata fita ya daure fuska yace "Ga Magani nn for the sake of Allah and Islam!" Kallonsa tayi da rinannun idonta sai kuma ta dau ledan ta fita daga motar saura kiris ta fadi amma hakan bai sa yace komai ba, tana layi ta nufi gate, yayi tsaki yayi reverse ya kwasa da gudu ya bar wajen, a daddafe ta isa bedroom dinta ba tare da ta yrda tayi ko wani kara da xai ja attention din mum dinta ba, ta jefar da ledan drugs din hannunta ta fada kan gado ta shiga juye juye hawaye na sakko mata. 📚✍🏻 [7/19, 5:58 AM] 0mmer Farouk: 💫 *Noorul Huda*💫 2...... Yana gama parking a space din da aka tanadar don yin hakan a gidan ya bude mota ya fito, kalle kalle ya dinga yi kafin ya xaga xuwa gun shan iskan dake gidan ya ciro kwalin cigarette a aljihunsa da lighter ya ciro stick daya ya kunna mata wuta ya hau zuka, stick biyu ya gama da cikin d'an kankanin lkci ya mayar da sauran aljihu snn ya mike ya koma gun motarsa ya bude ya fito da wani abu kamar turare ya feshe bakinsa da shi ya mayar ya kulle motar snn ya shiga gida cike da tafiyarsa ta kasaita, a hankali ya murda kofar parlor ya shiga ya rufe a nutse yanda baxa a ji ba yana kallon agogon dake manne parlon yaga har karfe daya, xaro ido yyi da mamaki, how time flies, yaushe ya ajiye yarinya snn yaje gidan frnds dinsa suka tafi club amma har lkci ya wuce haka bai sani ba, stairs ya nufa yana tafiya a hankali kada ma aji footstep dinsa, yana isa corridor din rooms aka bude wani kofa, wata dattijuwa da baxata wuce 50 da wani abu ba ta fito tana kallonsa, wara ido yayi yace "Mamiiii!" Ta karaso inda yake bbu yabo bbu fallasa tace "Daga ina kake Abuturrab?" Ya shiga sosa kai yace "Am Mami daga clinic nake ban gama aiki da wuri...." Ta girgixa kai tace "Karya kake!" Shiru yayi bai ce komai ba, Cike da damuwa Mami tace "Yanxu Aliyu baxa ka ma kanka fada ba, it's high time fa kasan inda ke maka ciwo, banda bin mutanen banxa bbu abinda ka iya a rayuwa, what's the use of this, me yasa baxa ka bar ni in huta bane a rayuwar nan, idan kanninka suka yi kuma kace me?" Shiru yayi ya sinnar da kai bai ce komai ba, ta karasa gabansa kamar me son gano abu, ya rike breathe dinsa da sauri, ta kamo hannunsa ta kai hancinta ta girgixa kai tace "Ae shknn, continue destroying ur life, ur being an only son does not mean u are an only child...." Ya marairaice yace "Plss Mami am sorry...." Tsawa tayi masa tace "Shut ur mouth!" Yayi shiru yana kallonta ta juya ta shige bedroom dinta ta rufe kofar, ajiyar xuciya ya sauke ya shiga dakinsa, bathroom ya fada yayi wanka ya saka sleeping robe dinsa ya kwanta, ji yyi cikinsa na kugi, sai a snn ya tuna ashe fa bai yi dinner ba, hamma yayi ya mike xaune, tunanin abinda xai ci ya shiga yi, can ya mike ya nufi kofa ya bude a hankali ya nufi dakin sisters dinsa, a hankali ya tura kofar ya shiga ya rufe, ya lalubi switch din room din ya kunna, suna kwance su uku gaba daya sun yi bacci, ya karasa gadon ya xauna yana kallonsu, Ramlah ya shiga tashi a cikinsu ta bude ido da kyar tana kallonsa ya marairaice yace "Lil sis I've not eaten...." Hade rai tayi tace "Ohh yaya bacci fa nake xaka tashe ni.... Ga Leesah ka tashe ta mana" daga haka ta juya masa baya, kallon Khaleesat yayi ya shiga tashinta, ta mike xaune kamar xata yi kuka tace "What again ya Abuu?" Ya marairaice murya yace "Ban ci abinci ba fa" tsuke fuska tayi tace "Toh ni ba ni na raba abinci ba Mami ce, but you can ask Ilham" daga haka tayi kwanciyarta ita ma ta juya masa baya, ji yyi kamar ya kwada masu mari don dai dare ne kuma kada Mami ta juyo su, ya kalli Ilham ya shiga tada ta, ta juyo tana kallonsa yace "Pretty ban ci abinci ba fa" hade rai tayi ta mike xaune tace "Toh ba kai ne baka dawo da wuri ba, ni dai ya Turab ka daina tashi na idan ina bacci ba ga Anty Ramlah da Leesah ba...." Turo baki tayi ta sauko daga kan gadon tana gunguni ta fice daga dakin, duka ya d'ada masu su biyun suka mike a firgice ya hade rai yace "Duk xan yi maganin ku" daga haka ya mike ya fice daga dakin ya sauka downstairs, yana tsaye bakin kofar kitchen Ilham ta gama hada masa abincin nasa a tray ta fito ya bi bayanta suka koma sama, a dakinsa ta ajiye masa ya xauna gaban abinci ta nufi kofa xata fita sai kuma ta juyo tace "Baxa ma kace thank you ba ko" wani kallo ya jefa mata yace "Baxa ace ba" murguda baki tayi ta fice daga dakin. Washegari da safe da ya kasance Lahadi Abuturrab da wasu frnds na xaune gaban gidan daya daga abokin nasu Ayman street na uku away from gidansu Abuturrab din, Abuturrab ya kalli direction din da Saleem ke kallo ya hango wasu mata su uku suna tahowa, gaba daya abokan suka maida hankali gun matan, Abuturrab ya d'an yi tsaki ya dauke kai, har suka iso dai dai inda suke, Ayman yace "Cute!" Sai a snn Abuturrab ya juya yana kallonsu, ido hudu suka yi da ita, ya kasa daina kallonta ita ma haka kuma lkci daya ya ganeta, da alamar ita ma ta ganesa ganin kallon da take masa, da sauri ta dauke kai ta ci gaba da tafiya, Ita kadai ce me doguwar riga har kasa cikinsu amma sauran duk halve gown ne jikinsu, Basu wani yi nisa ba ta kalli kawayen nata tace "Kunsan me, shine guy din da nake gaya maku daxu, he rescued me..." Ta gefenta tace "Really? And you walked passed him baki masa magana ba" kamo hannunta dayar tayi tace "Gaskiya bai kamata ba ki koma ki masa godiya you don't have to pretend shi ma nasan ya gane ki" without a second taught ta juya da sauri ta nufe inda suke xaune, da sauri Abuturrab ya dauke kai, Salman yace "She's coming toward us fah" Salim dake ta kallonta da Ayman suka yi shiru har ta karaso, doguwa ce sosai kuma fara amma ba wani can ba, tana tafe ne kamar iska xae kade ta, yeah she's so beautiful kyau me daukar hankali kuwa, daga nisa ma kana iya ganin girman idonta da haskensa, tana isa inda suke ta tsaya tana kallon Abuturrab da alamar ta ma rasa abinda xata ce, sai fidgeting fingers dinta take cikin in ina tace "I I.... Came to thank you!" Kallonta kawai yake, ya kasa dauke kai, a hankali idonsa ya sauka kan abinda ke rataye a wuyarta wanda hakan sai da yasa gabansa ya fadi ba kadan ba, Salim ya take kafarsa yayi saurin dauke kai, sai kuma ya kalleta yace "Ki gode ma Allah!" Juyawa tayi ta bar wajen da sauri, abokansa suka bi ta da kallo har ta isa gun kawayen ta suka ci gaba da tafiya, Salim yace "Where did you know her?" Bai ce komai ba ya xaro kwalin cigarette ya ciro daya da lighter ya kunna ya kai baki. Tana isa gida ta tadda Mum dinta na tare da baki a parlor ta gaida su da ladabi snn ta wuce sama xuwa dakinta ta jefa jakar hannunta ta shiga toilet tayi wanka ta fito ta fiddo kananun kaya ta saka ta kwanta, lkci daya ya fado mata, sai a snn taji haushin kanta da taki barin wajen bayan ya shareta, tayi tsaki ta rufe fuskarta da pillow, har ta fara bacci taji muryar mum na kiranta, ta mike xaune da sauri tana mitsike idonta, Uwar tace "Samantha ki fito ga abinci can a dinning, baxa ki Catechism bane?" Tace "Mumy da rana fa yau" hade rai Mumy tayi tace "Kina da hankali kuwa, ranan ne xai hanaki xuwa? C'mon my frnd tashi ki shirya and get out of this house, mates dinki a karkashin wata suke tafiya ba ranan ba?" Daga haka ta fice daga dakin, Mikewa Samantha tayi ta sauka parlor a sanyaye, xaune ta ga dad dinta a d'an study area yana sanye da medicated glasses dinsa, Holy Bible ne gabansa yana karanta wa, karasawa tayi inda yake ta masa side hug bai ce komai ba gaba daya attention dinsa na kan Bible din, murya can kasa tace "ina yini Abbana" kai kawai ya gyada mata ta nufi dinning ta debi abincinta ta xauna nan ta ci, sannan ta koma sama ta shirya cikin wani gown din tayi rolling kanta ta fito rike da bible dinta da Hymn book, dakin Mumy ta shiga ta ganta tana ta shirin fita fellowship ita ma, ta karasa tace "Mumy sai na dawo!" Mumy tace "Alryt dear, kila baxan dawo yau ba sbda vigil da xa muyi, you take of yourself, ga transport din ki a gaban mirror na aiki driver" Samantha ta d'an bata fuska tace "Har da Abba?" Mumy tace "Nooo shi yana gida bbu inda xa shi, xae yi bak'i anjima" juyawa Samantha tayi tace "Ohk bye!" Daga haka ta fita bayan ta dau kudin, da kafa take tafiya har tayi nisa sosai tayi deciding ta bi layin gidansu class mate dinta Esther su tafi church din tare, tafiya take tana d'an wake wakenta, tayi nisa sosai don bai wuce gida hudu xata wuce snn ta sha kwanan gidansu Esther ba, gabanta ya fadi ganin wanda ta gani tsaye jikin motarsa a gaban wani gida ga wata yarinya na tsaye daga kusa da shi, kamar ance ya daga ido suka yi ido hudu, da kyar ta bude baki tace "Ina...ina yini!" Yace "Lafiya lau" daga haka ta wucesa, yarinyar ta bi ta da kallo snn ta kallesa tace "Waye ita Aliyu?" Da kamar baxai ce komai ba, sai kuma yace "A frnd!" Ta tabe baki tace "A Christian frnd?" Bude motarsa yayi ya shige ta koma baya da mamaki tana kallonsa tace "Abuturrab?" Ta glass yake kallonta yace "Even if she's a pagan (Mara addini) it's non of ur business!" Tada motar yayi ya ja ya bar ta nan tsaye ta bi sa da kallon mamaki, can ta juya da sauri taga har Samantha ta bace, a fusace ta shige gida. Abuturrab na isa gida misalin sha biyu na dare yayi parking ya fito ko ba a gaya masa ba yasan Abba ya dawo ganin Prado dinsa, bae ko kalli sojojin dake tsaye ta ko ina a compound din ba ya shiga parlor Ramlah ta leko daga kitchen murya can ciki tace "Ya Abu Abba yana neman ka..." Yayi mamakin ganinta a kitchen a wnn lkcn gashi bai ji mai take cewa ba ma, xai karasa inda take suka ji muryar Mami tace "Kina da hankali kuwa Ramlah" juyawa tayi da sauri ta koma kitchen, hade rai yayi ya gaisheta shi kenan kullum cikin laifi kuma sai yayi ta xaman gida kamar mace, infact mayar da duty dinsa na clinic xuwa dare ma xai yi kawae, Mami ta amsa gaisuwarsa ba tare da ta kallesa ba xai haura sama sai ga Abba ya fito daga parlonsa, tsaye yayi gabansa na faduwa ya d'an risina ya gaishesa Abba yace "Daga ina kake Aliyu?" Sunkuyar da kai yyi ya ma rasa abinda xai ce, can dae yace "Abba taimako na tsaya yi a....." Abba ya girgixa kai yace "No! You can't just be coming into my house when ever you wish at any time, don haka ka tattara inaka inaka ka koma boys quatr snn ka bude gate din can kaga idan yaso ko da yaushe ka ga dama xaka iya shiga ka fita bbu wanda ya sani, bbu wanda kuma xai hanaka, do what I say immediately now, stupid you!" kansa a kasa yace "Toh Abba, Allah ya huci xuciyar ka" Ramlah ta karaso parlon kamar xata yi kuka tace "Abba pls forgive him for the last..." Wani kallo ya mata ta juya da sauri ta koma kitchen, Abuturrab ya haura sama ba a dau lkci ba ya fito da jakunkunan kayansa da komai nasa da xai bukata, har lkcn Abba na tsaye parlor haka ma Mami da bata ji dadin hukuncin ba, Fita Abuturrab yyi ya kira mai gadi ya taya sa daukan kayan, tsakanin main gidan da boys quatr ba wani tafiya bane can, sai dai ba lallai ka ma san me ke faruwa can ba barin ma da Abba yace ya bude gate din can, cikin yan minutes ya gama mayar da kayansa can snn ya koma yayi ma parent din nasa sai da safe ya dawo, dariya ya dinga yi shi kadai a parlor yana tafa hannu ya fada kan kujera yace "Waow waoww enough privacy!" ya mike yana murmushi ya shiga inda dakuna suke ya xabi wanda yake so ya shigar da kayansa, ya dau lkci sosai yana gyaran dakin sbda kura don ba a fiye amfani da wajen ba sai dai a sauke baki, Abuturrab ba dai tsafta ba cikin few hours ya tsaftace dakin da bathroom ya kure Ac ko ina ya dawo yana kamshi ya shimfida bedsheet, snn yayi kwanciyarsa don ya ci abinci a waje, nan da nan bacci ya daukesa, washegari Monday yana shirin fita office aka danna bell daga waje ya karasa ya bude, Cook ne rike da tray din breakfast dinsa ya d'an bude ido yace "Ohh I thought girkin ma nan xa a dawo yi min" cook din dai bai ce komai ba ya gaishesa Abuturrab ya karbi tray din yace "Thanks" har ya tafi ya kirasa ya basa spare key din parlon yace "Gashi ko bana nn idan ka kawo min abinci ka shigo kawai ka ajiye" Cook din ya karba da ladabi yace "Ohk sir" daga haka ya juya ya wuce shi kuma ya koma ya ci gaba da shirinsa snn ya yi breakfast ya dau makullin motarsa ya fita, main house ya nufa ya gaida Mami ta amsa tana kallonsa tace "Hope you are now satisfied with the punishment?" Murmushi yayi yana shafa kai Mami tace "Ka canxa halin ka Abuu, you are grown up fa yanxu, soon xa ka ji Abba ya fara maka maganan aure idan kuma kaki fidda mata na tabbata fiddo maka ita ba wahala xai masa ba, you are 30 yanxu amma kaki nutsuwa ka san inda ke maka ciwo koh" murmushi yayi yace "Mami ni fa ba dauko maku magana nake ba, ba sata nake ba, ba kisa nake ba, kuma... Um Mami ni bana neman mata kin sani fa!" Bude baki tayi da mamaki tace "Ehh lallai Aliyu ashe baka da kunya..." Dariya yayi yace "Allah Mami, naga wa ennan sune rashin jin, kuma duk bana yi" harara ta 6alla masa tace "toh shaye shayen fa da bin abokan banxa" xaro ido yayi ya dawo kusa da ita yace "Ohh Mami wllh ni na bar wannan abun da dadewa bana shan komai yanxu" wani kallo tayi masa tace "Cigarette din fah?" Ya sosa kai yace "Uhm Mami shi ma ina kkrin in ga na daina wllh, just continue praying for me" ta shafa kansa tace "Toh Allah yasa haka son. Be a good man plss, sannan ka canxa abokan ka" mikewa yayi yana murmushi yace "Toh Mamina na tafi aiki...." Daga haka ya fita da sauri ya nufi parking lot, yana shiga motarsa ya bar gidan, dai dai traffic kamar ance ta juya ya ga Samantha a bayan mota sanye da uniform alamar sch xata, mamaki ya cikasa, why yake haduwa da ita frequently now, bayan ko taba ganinta bai yi ba kuma daga layinsu xuwa nasu gidan bbu wani nisa can amma bai taba lura da ita ba, ita ko ganin yanda yake kallonta ta daga masa hannu hade da yin murmushi, murmushin ya mayar mata ya gyada mata kai snn ya ja motarsa don an basu hannu ya dau hanyar gun aikinsa. 📚✍🏻 [7/19, 5:58 AM] 0mmer Farouk: 💫 *Noorul Huda*💫 3...... Karfe biyar saura Samantha ta dawo sch, duk da driver ne yaje daukota amma a titin anguwar tasu ya ajiyeta wai xai je dauko Mumy daga church, yawanci a nan take yawan sauka sai dai ta karasa da kafa, tafe take jakarta a bayanta da ganinta kasan a gajiye take, wani mota that look familiar ne ya xo ya wuce a guje ta bi motar da kallo, bai yi wani nisa ba taga kuma ya tsaya, ita dai tafiyarta kawai take, a hankali ya dinga dawowa baya har ya iso inda take ya sauke glass, d'an bude ido tayi ganin wanda ke cikin motar, kafin yace komai tace "Good evening," yace "Evening, let me drop you" kai ta gyada masa ta karasa ta bude front seat ta shiga ta rufe sannan ya ja motar, bai ce mata ba ita ma haka sai dai ynxu kam ba gudu yake ba, ji tayi yace "Ur name?" Ta kallesa tace "Samantha!" Ya d'an kalleta snn yace "Samantha?" Tayi murmushi tace "Samantha David!" Ya gyada kai yace "Nyc!" Tace "Urs?" Kamar baxai ce komai ba sai kuma yace "Aliyu Ahmad!" Murmushi tayi tace "Nyc name," kallon Stethoscope din dake sakale gaban motar tayi tace "You are a doctor?" A takaice yace "Yes" bata kuma cewa komai ba har ya iso gaban gate din gidansu ta kallesa tace "Thank you" yace "Welcm" har xata fita sai kuma ta tsaya ta kallesa tace "Every doctor can draw perfectly, will you pls help me draw the Diagram of the Mammalian heart and Human Skeleton?" Kallonta ya tsaya yi, can yyi Murmushi da ya bayyana light dimple dinsa yace "Really? To ni ban iya ba" kamar xata yi kuka tace "Allah nasan ka iya Plss ka min mana" shiru yayi yana kallon yanda karamin bakinta ke motsi sai kuma yace "Ohk," cike da murna tace "Ohk to bari in dauko materials din" dakatar da ita yayi yace "Am exhausted I can't wait, idan mun sake haduwa sai ki ban" daga haka ya daga mata hannu ya ja motar ta bi sa da kallo, cikin minti biyar ya isa nasu gidan ana bude masa gate yayi parking har xai nufi kofar main parlor ya tuna ai fa ya koma Boys quatr ynxu, dariya yayi ya nufi can, wanka kawai yayi ya dawo ya debi abincinsa dake ajiye snn ya ci ya kwanta don ya gaji sosai, shidda saura ya mike ya fita ya xaga boyz qtrs din gaba daya, ya bude gate din da Abba yace, ya fita waje da farin kujera ya xauna yana kare ma street din kallo don sai yyi shekara bai bi nn ba duk da bayan gidansu ne, baxa ka taba cewa akwai mutane unguwar ba tsabar shiru, tafe suke su biyu da alamar sun dawo daga church ne, tun daga nisa ya gano ta ta yanda take tafiya, haka ya dinga kallonsu har suka karaso, ta xaro ido ganinsa tace "Doctor!" Wara ido yayi bai ce komai ba ta karasa kusa da shi da sauri ta sauke jakar dake goye bayanta ta fito da materials din drawing din ta mika masa tace "Na kama ka" murmushi yayi ya karba yace "Nawa xa ki biya?" Ta langwabar da kai tace "Ko nawa, amma service before payment" dariya yayi wanda hakan ya fito da ainahin kyansa na d'an pillo, ya kuma bayyane fararen set din hakoransa masu daukar ido, shiru tayi tana kallonsa, yace "Ke me wayo ko?" Murmushi tayi tace "nan ma gidan frnds din ka ne?" Ya girgixa kai yace "Gidanmu ne" bin gidan tayi da kallo tace "Da gaske?" Yace "Yeah!" Tace "Hmm Ohk, to yaushe xan karbi xanen?" Yace "Ran da na gama" tace "Noo we are submitting it as test on Wednesday" yace "Ohk, xan yi anjima" tace "Yauwa na gode bye" daga haka ta nufi mai aikinsu blessing dake jiranta. A ranan da daddare Abuturrab ya xauna misalin karfe goma a gun da ya tanadar as study room, ya bude textbook din da ta basa domin Duba xanen a jiki ya kwafa, tabe baki yyi ya rufe, lumshe ido yyi na kusan minti biyar yana nazarin diagram din heart a xuciyarsa, can ya bude ido ya dau well sharpened pencil din ya shiga xana Big Mammalian heart gwanin ban sha'awa ko wani curve ya basa hakkinsa, sosai Heart din ya xanu yyi kyau kamar drawing din Artist, cikin few minutes yayi labelling ko ina snn ya ajiye pen din ya lumshe ido yana nazarin skeleton, bude idon yyi ya bude wani page ya shiga rangada babban xanen Human Skeleton, ko wani k'ashi sai da ya tabbatar ya xana, ya gama tsaf snn yayi labelling ya gama ya rufe book din yana hamma ya mike ya shige bedroom ya fada kan gado sai bacci. Washegari da xae fita aiki bae bari ya mance materials dinta ba in case ko xa su hadu, ya ajiye back seat snn ya bar gidan bayan ya shiga ya gaida Mumy, amma bai ganta ba ranan, da ya baro gun aiki ma haka ya dinga dube dube a hanya ko xai ganta amma har ya isa gida bai ganta ba. Karfe takwas na dare ya shirya ya fita hankalinsa kwance ta gate dinsa bbu wanda ya sani bare yyi querying dinsa inda xa shi, gidansu Saudat ya nufa don yyi missing dinta tsakanin jiya da yau, yana isa ya kirata, ba a dau time ba ta fito sai dai kumbure kumbure kawae take, yyi murmushi yace "Why the pouting?" Ta hararesa tace "Ka manta bari na tsaye kayi ranan ka wuce?" Kamo hannunta yayi yace "Ohk Am sorry dear, how you doing?"ta turo baki tace "Am good" ya shafa kansa yace "So what's new?" Tace "Baxa ka shiga ciki ba?" Yace "Noo, an san kin fito ne?" Tace "Just my little sis" yace "Mum fah?" Tace "She's in her room" yace "Toh rakani mu je mu dawo yanxu" tace "No the other time I escorted you ka sa ana ta min wani kallo a club ni baxan je ba" ya wara ido yace "Wa yace maki can xan je?" Ta hararesa tace "Ban san ka bane" dariya yayi yace "Plss baby we are not staying long fa kawai rakani xa ki yi Akwae abinda xan karba ne" shiru ta d'an yi, sai kuma a hankali tace "Ohk, just thirty minutes before ayi noticing bana gida" hannun ta ya kamo yace "Ohk dear" daga haka ya tada motar ya dau hanyar club din nasu, duk da bin sa da Saudat take club kaffa kaffa take da kanta kuma bata sake ma kowa fuska, don tana mugun sonsa shi yasa bata iya kin yin abinda yake so, Saudat kyakkyawa ce ta ajin karshe, irin matan da samarin xamani ke so, Abuturrab bai yi amfani da wnn advantage din son da take masa ba ya cutar da ita, iyaka kawai ya rike mata hannu sae d'an peck, coz he always keep it at the back of his mind dat shi ma yana da k'anni mata, bai kuma son komai ya samu lovely sisters dinsa, hakan yasa yake yaki da duk wani yaudara na diya mace, kafin minti talatin din kuwa ya maida ta gida bayan sun shiga eatry ya cika ta da kayan ciye ciye, ba shi ya koma gida ba sai kusan sha daya sai a snn ya kuma farin cikin basa side dinsa da Abba yyi, ynxu bbu wanda xai ma san ya dawo bare yace daga ina yake, yana parking gaban gate din ya fito xai bude don bbu mai gadi a side din kuma bai ma bukata, yana bude gate ya dawo xai shiga motar ya hango Samantha da wata mata da baxata haura 40 ba, wai! Da ganinta kaga rikakkiyar Christian, skirt ne jikinta shi bai kai kasa ba amma dogo ne sosai, sae wani bujejen riga da tasa tayi tuck in dinsa cikin rigar, kanta na sanye da irin hulan nan nasu na pastress, hannunta dauke da wani gundumemen Bible, dayan kuma na rike da hannun Samantha, da ganinsu kasan daga church suke, Samantha da ta gansa ita ma sai kallonsa take fuskarta dauke da murmushi har suka iso dai dai inda yake, satan kallon uwarta tayi taga hankalinta na gaba sai rera worship songs take, hannu ta daga masa a hankali alamar bye bye, ya sakar mata murmushi shi ma ya daga mata hannun, har suka wucesa bin su yake da kallo, doguwar riga ce jikinta sai rolling da tayi a kai, girgixa kai yayi ya shiga motarsa ya ja xuwa ciki yyi parking snn ya dawo ya rufe gate din, wanka yayi ya jima xaune yana karatun Qur'ani daga karshe ya mike ya shiga bedroom ya d'an yi xuke xukensa snn ya kwanta. Washegari da ya kasance laraba ana idar da Sllhn Asuba a masallaci drawing din Samantha ya fado masa gashi tace ranan xata yi submitting kuma test dinsu ne, satan kallon Abbansa dake Azkar yyi, don kusan ko da yaushe tare suke fitowa daga masallaci, kuma yasan ynxu sai ya bata rabin awa yana xaune, fuskewa yyi ya mike ya fice ya nufi gida, tsaye yyi a balcony yana tunanin ko dai ya bari kila idan xai fita aiki su hadu, sai kuma ya tuna jiya ma through out basu hadun ba, ya shiga gida ya dauka makullin motarsa ya fito ya bude motar ya dauki littafin da textbook din sai math set ya bude gate ya fice, tafiyar minti goma yayi ya iso dai dai gate dinsu, rasa yanda xai yi yyi, gashi har lkcn gari bai gama washewa ba, bai ma ga alamar an bude gate din nasu ba, leken cikin gidan ya shiga yi yaji daga bayansa an daka masa tsawa "Heyyy who you be, who you find?" Juyawa yyi da sauri yana kallon mutumin ko ba a gaya masa ba yasan mai gadin gidan ne, yace "Ehm, Samantha!" Mai gadin ya masa wani kallo yace "Wetin do Samantha?" Mika masa abubuwan hannunsa yayi yace "Give her plss" daga sama har kasa mai gadin ke kallonsa, Abuturrab ya kalli kansa, jallabiya ce milk colour jikinsa, karasowa mai gadin yyi yace "Who make I say?" Abuturrab yace "Aliyu!" mai gadin ya sa hannu ya karba Abuturrab ya juya ya bar wajen, karfe bakwai da kusan rabi yana kkrin rufe kofa Ilham ta karaso, ya juya yana kallonta yace "Pretty!" Tace "Ya Abu ko shigowa ka daina yi dama nasan kafi son haka" dariya yayi yace "Eh mana, baxa ku ma dinga gani ba bare ku dinga yangan bani abinci na" tace "Yaya pls ka ba Abba hakuri ka dawo cikin gida we are missing you" kamar xata yi kuka ta kare maganar, yace "Noo, I like it so much here" tace "Why?" Yace "Nothing" tabe baki tayi tace "Ae shikenan, kayi breakfast?" Yace "Yep, Peter ya kawo min" daga haka ya kama hannunta suka bar wajen yace "Za ki sani latti, ki sa kanki latti" tace "Ya turrab 5k plss" yace "I don't have cash, sai ltr" bai jima gun Mami ba ta fito ya hau motarsa xuwa gun aiki. Da ya tashi dawowa da yamma daga gun aiki da gundumemen K'arensa ya dawo da cage tare da mutumin dake rike da Karen, cikin few minutes aka hada cage din karen mutumin ya fito da karen da bakinsa ke a daure ya turasa cage ya rufe snn ya kunce mouth cuff din dake bakinsa, nan karen ya hau haushi, Abuturrab yyi murmushi yace "Yesss!" Tap ya nufa ya bude ruwa yana wanke hannunsa sannan ya dawi yana kallon mutun yace "Yanxu ya xa ayi karen ya saba da ni?" Mutumin yace "In dai kai ne xaka dinga basa abinci ko da yaushe cikin lkci kankani xai saba da kai" Abuturrab yace "Ohk nagode" nn ya sallami mutumin ya basa kudin mota, yana tsaye yana kallon katon karen da ya fito da halshe sai hakki yake ya ji muryar Mami a bayansa, juyawa yayi da sauri da mamaki tace "Meye wnn kuma Abuturrab?" Wara ido yayi yana murmushi yace "Dog Mami!" Hade rai tayi sosai tace "Uwar me yake a gidan nan?" Ya marairaice yace "Mami gadi xai dinga min ni bana son mutum nafi son dabba!" Bude baki tayi tana kallonsa, can ta girgixa kai tace "Toh ba gidan nan ba kare xai maka gadi, sai ka jira idan ka koma gidan ka na kanka!" Yace "Nooo Plss Mami, bangarena ne nn fah!" Tace "Nace ka fitar min da wnn abun Aliyu" karasowa yyi kamar xai yi kuka ya mata side hug yace "No plss Mami, kinga fa ina jin kamar jiya barayi sun xo anguwar nn, pls ki bar min karen it will be a good watch man for me, bbu abinda masu gadin nn suka iya sai bacci...." Girgixa kai tayi ta juya ta fara tafiya tace "Ni dai bbu ruwana...." Murmushi yayi yace "Yes Mami" main gidan ta nufa ba tare da ta tanka sa ba. Yana xaune misalin biyar kan farin kujera yana danne dannen wayarsa yaji kamar motsi jikin gate, ya daga kai da sauri, sai kuma ya mike ya nufi gate din ya bude, tsaye ya ganta kamar munafuka, tana ganinsa ta koma baya a tsorace, murmushi ya sakar mata murya can kasa yace "Samanth....." Sai kuma yyi shiru a hankali yace "Samha!" Wara ido tayi tana murmushi tace "Ashe kana nan, just came to say a big thank you!" Har da d'an risinawarta ta kare maganan, ya jingina jikin gate ya rungume hannayensa yana kallonsa yace "For what" turo baki tayi tace "For the beautiful drawing mana" Murmushi kawai yyi yana kallon hannunta dake dauke da Bible, mota ce ta shawo kwanan anguwar ta juya da sauri tana kallon direction din, ta xaro ido tace "Jesus! Abbana ya dawo" kallon motar yayi da sauri sai kuma ya matsa daga gun gate din bata jira yace mata komai ba ta shige cikin gidan, wara ido yayi yana kallon motar har ya xo ya wuce snn ya shiga gidan ya rufe gate din, tsaye ya ganta tayi lamo jikin flower, tana ganin ya rufe gate din ta karaso da sauri tace "Ae ya tafi ko, let me leave" kallon gate din yayi yace "I don't think ya tafi fa, tare yake da wasu a motar kuma na ga sun tsaya" kamar xata yi kuka tace "Bbu wani hanyar doctor?" Girgixa Kai yayi yace "Only this.... Ga kujera ki xauna ki jira su wuce sai ki tafi," Da damuwa tace "Church fa xan tafi, I don't want to miss" shiru yyi yana kallonta, can ya juya ya dau wani kujerar yayi xamansa, bin bayansa tayi tana bin gidan da kallo ta xauna kujerar da ya nuna mata tace "Are you the only one leaving here?" Girgixa kai yayi ya nuna mata hanyar da main house din yake yace "My family members are there, my Mum, Dad and sweet siblings" mikewa tayi ta nufi inda ya nuna mata bata wani yi nisa ba ta hango kantamemen gidan daga nisa, dawowa tayi da sauri tace "Uhn! Toh me yasa kai kake boys quatrs?" Murmushi yayi yace "Because I am a boy, an I prefer here" 'yar dariya tayi tace "Ohk that's true, xan wuce church yanxu" mikewa yayi yace "Bari in duba maki ko ya tafi" daga haka ya tafi gun gate ya bude ya leka, rufewa yyi da sauri ya dawo yace "Noo they are still there ki xauna kawai su wuce" bata fuska tayi tace "Lokacin Church na wucewa" bai tanka ta ba hakan yasa ta xauna, haushin k'are taji ta mike a firgice tana kallon direction din, ihu tayi suna ido hudu da katon karen ta juya xata gudu a rikice yyi saurin rikota da sauri, ta fashe da kuka tace "Noo bana son kare pls" xaunar da ita yyi kan kujera ya durkusa gabanta yana kallonta yace "But it's caged" Har lkcn jikinta rawa yake ta kasa cewa komai, dagota yyi ya shiga balcony da ita ya sa ta xauna ya duka gabanta yace "Ohk sorry Plss...." Hawaye ya sakko idonta tace "Ni xan tafi" mikewa yayi ita ma ta tashi, yace "Karen baya komai, it's very frndly" bata ko kalli inda karen yake ba ta nufi gate da saurinta, ya bi bayanta amma tuni ta fice, tsaye yyi bakin gate dinya rungume hannunsa ya bi ta da kallo ganin yanda take sauri, sai da ta tabbatar tayi nisa snn ta juya ta kallesa, d'aga masa hannu tayi, ya juya ya shige gate din yayi banging dinsa, kasa ci gaba da tafiya tayi sai kallon gate din take, can ta juya jiki ba kwari ta ci gaba da tafiya. 📚✍🏻 [7/19, 5:58 AM] 0mmer Farouk: 💫 *Noorul Huda*💫 4...... Washegari da yamma misalin biyar da rabi Abuturrab na xaune karkashin artificial bishiyar dake dauke da fararen kujeru a karkashi hannunsa rike da Cigarette, dawowarsa kenan daga aiki yayi wanka ya d'an tsakuri abincinsa da ke ajiye a parlor snn ya fito ya xauna ya fara aikin xuke xukensa idonsa na kan k'aren dake ta fama da gundumemen naman da ya siyo masa a hanya, murmushi yayi ya mike ya shiga ciki sai ga shi ya fito da babban drawing board da materials din drawing dinsa, bude board din yyi ya tsayar ya dawo da farin kujera kusa da board din ya xauna dai dai yanda xai dinga ganin karen da kyau, ya fi minti biyar yana kallon karen hannunsa rike da well sharpened drawing pencil din hannunsa, daura hannun nasa yyi kan board din, a nutse ya shiga xana k'aren, ya kusa minti goma yana xana kai snn ya dawo jiki, yyi rabi yaji an tura gate a hankali ya juya da sauri, ido hudu suka yi da ita, ta wara ido kamar mara gaskiya ta k'asa tsaye gu daya tana jujjuya Bible din hannunta tace "Am... Ina yini!" Murmushi yayi ya maida dubansa kan board din gabansa yace "Come in....." Kin shigowa tayi tana yi tana lekan karen dake cage tace "No, am going for service!" Ya kalleta yace "Ohk baxa a gaisa ba knn yau?" Murmushi tayi tace "Gashi na gaishe ka, and I can see you are busy drawing what I can't see from here!" Mikewa yayi ya karasa gabanta, tayi tsuru tsuru tana kallonsa, kallonta yayi daga sama har kasa, yau ma doguwar riga ce sea green jikinta, sai jan veil da ta daura a kanta, cikin idonta dake kyalli kmr ta tara hawaye ya kalla, ta juya da sauri xata bar gate din ya riko hannunta, juyowa tayi tana kallonsa, ya sakar mata murmushi yace "Yea, baxa ki ga abinda nake zanawa daga nan ba sai kin shigo" kallon karen tayi a tsorace tace "Noo, ni ina jin tsoron...." Jawota yayi xuwa cikin gidan ya rufe gate din, tace "Noo Plss...." Janta yyi har xuwa gun drawing board din sai buya take bayansa, ya dawo da ita gaba idonta ya sauka kan xanen, shiru tayi tana kallo ko kiftawa bbu, a hankali ta furta "Waoww....." Kallon karen dake cage tayi snn ta kalli na drawing din ta juya da sauri tana kallonsa tace "Doctor wa ya koya ma drawing haka, you are.... " Rungume hannayensa yayi yace "In koya maki ne ke ma?" Da sauri ta gyada kai, ya ja kujeran ya xauna ya dau pencil din ya ci gaba da xanen, durkusawa tayi a hankali kusa da shi ta dafa kafarsa tana kallon yanda yake xanen cike da kwarewa, muryar Khaleesat ya ji, ya juya da sauri sai kuma ya mike ya xaga ae ko ya hango ta ita da Ilham suna tahowa, dawowa yayi da sauri yana kallon Samantha tun kan yace komai ta mike a rikice tace "Your sister I guess?" Bai ce komai ba ya kama hannunta ya nufi kofar parlor ya bude ya sa ta shiga snn ya rufe ya dawo gun drawing din ya xauna ya ci gaba, Khaleesat da Ilham suka karaso, Ilham ta wara ido tace "Waow ya Abuu.... It's sooo beautiful!" Ta gefen ido ya kalleta yace "Thanks" Khaleesat ta durkusa kusa da shi tace "Yaya wai Anty Ramla tace kace xaka kawo wani karen main house, da gaske ne" ya hade rai yace "You two can see am busy...." Khaleesat tace "Don ma mun taho taya ka hira tunda bbu islamiyya yau?" Bai tanka ta ba, Ilham tace "Toh shknn since he's busy let go inside and....." Mikewa yayi da sauri kmr wanda aka mintsila yace "Go where? Kar warce ta shigar min parlor....." Ilham ta bude ido da mamaki tace "Why?" Wani kallo ya watsa mata ya nuna mata hanyar inda suka fito, ganin bbu wasa tattare da shi yasa duk suka juya suka bar gun, ya bi su da kallo har suka bace, ya ajiye pencil din hannunsa, Samantha dake ta kallonsu ta window ta bude kofa ta fito, murmushi ta masa tace "Ur siblings are cute, they re fine...." Rungume hannuwansa yayi ya daga kafada, tace "Bye na tafi church!" Daga haka ta nufi gate ya bi ta da sauri yace "Wait! Baxa ki jira in gama ki gani ba" tace "Lkci na wucewa xan je church ne fa" yace "Ohk I will be very fast sai ki wuce" shiru tayi ya wara mata ido yace "C'mon" karasowa tayi ya xauna ya ci gaba da drawing din ita kuma ta durkusa kusa da shi, sai da aka yi wani minti talatin kafin ya gama xanen, ta xuba ma board din ido tana kallon katon karen dake ta dambe da k'ashi, can ta lumshe ido a hankali tace "Waow, you are so talented" murmushi yayi yana nodding kai yace "Thank you.... Samanth.. Uhm Samha!" Xaro ido tayi tace "Am not Samha but Samantha!" Ya daga kafada yace "Ohk all same...." Hamma yayi yana stretching din hannunsa yace "Am exhausted, No am hungry rather" tace "Baka ci abinci ba?" Langwabar da kai yayi yace "It's finished...." Shiru tayi sai kuma tace "toh me xaka ci?" Ya juya manyan Eye balls dinsa yace "May be black tea, da yaji kayan kamshi" ta tallabi kuncinta tace "Toh wa xai ma, ko xaka shiga gida ka gaya ma Mumy" ya d'an marairaice yace "She won't, yanxu dinner take yi na sani" a hankali tace "Toh ni in maka?" Yayi shiru sai kuma yace "Yess Plss" mikewa tayi tace "Toh xo ka nuna min kitchen din da komai...." Mikewa yayi yace "Yauwa thanks frnd, shiga ki jira inje can cikin gida in dauko lipton din da scent ingredients" dariya tayi tace "Ohk ohk" yayi murmushi ya juya ya nufi can cikin gida ita kuma ta shiga parlonsa, ba a dau lkci ba ya dawo rike da su a wani bowl, ta mike daga xaunen da take ta karba ya rakata kitchen din, yana tsaye daga bakin kofa ta gama dafa ruwan lipton din da ya dume gidan da kamshi, ta juye masa a flask din da ya nuna mata ya karaso kitchen din yana murmushi yace "Waow thanks frnd!" Murmushin ita ma tayi yayi mata stretching din long fair hand dinsa me dauke da kwantancen bakin gashi, a hankali tayi stretching din nata ya karba yayi shaking dinta, yana kallon kwayar idonta. Fitowa yyi da flask din parlor da cup, ta dau Bible dinta tana kallon agogo taga shidda har ya wuce kmr xata yi kuka tace "Ka ga har lkci ya wuce koh?" Da damuwa yace "Ayya, am sorry...." turo baki tayi tace "Yanxu I've missed church sai gobe kuma" yace "Toh ae nace am sorry, ki xauna in sha lipton din kad'an sai in raka ki har kofar gidan ku" xaro ido tayi tace "Dare xai yi" ya hade gira yace "Ba fa pounded yam nace xanci ba" murmushi tayi tace "Ohk ohk, I will wait" daga haka ta xauna ya dau cup ya bude flask ya debi lipton din ya kai lips dinsa, xaro ido tayi tace "Xai kona ka fa" dariya yayi yace "Na fi ki sanin haka" turo baki tayi ta dau Bible dinta ta bude tana kallo, da ta daga kai sai su hada ido, sun yi hakan ya kusa sau uku, yayi murmushi yace "Why you staring at me?" Kafin ta ce komai yayi saurin karawa da cewa "What are you reading" tace "Uhm! Holy Bible" shiru yyi yana kallonta can yace "Toh karanta min nima in ji" ta wara ido tace "Da gaske?" Ya gyada kai ta mike ta dawo kusa da shi da sauri ta xauna a kasa tace "Ohk I will, give me ur attention" kai ya gyada mata yana kallonta, verse din da chapter ta fado masa snn cikin sanyayyan muryarta ta fara karanto masa content din chaptern tana masa explain, kallonta kawai yake cike da tausayi, can ya lumshe ido ya ci gaba da shan lipton dinsa yana saurarenta, haka ta dinga karatun har ya ji kiran sallah, da sauri ya bude ido yana kallonta yace "Alryt, let stop there for today!" Tayi murmushi tace "Ohk!" Mikewa tayi tace "It's almost dark, xan wuce" yace "But nace xan raka ki ai, ki jira in dawo Masallaci" kamar xata yi kuka take kallonsa, can a hankali tace "Ohk!" Ya mike ya mika mata empty cup din hannunsa yace "Ke ma ki xuba ki sha" ba musu ta karba, ya nufi toilet din parlon ya dauro alwala ya fito yace "will be ryt back! You can lock the door kafin in dawo" Bin sa tayi da kallo har ya fita snn ta mike ta kulle kofar ta dawo ta xauna ta debi lipton din kadan ta sha, snn ta kai sauran kitchen, bin kitchen din ta dinga yi da kallo ganinsa fes kamar da mace a part din, fitowa tayi parlor shi ma ta dinga bin da da kallo can ta juya ta koma kitchen ta dauko sweeper da mopper ta dawo, tattare parlon tayi cikin yan mintuna don ba wani dirt bane a ciki snn ta hada ruwa ta sa freshener din da ta gani ta shiga mopping din parlon, tana gamawa ta goge kayan wutan gaba daya cikin mintunan da basu wuce talatin ba ta gama komai ta mayar inda suke snn ta dawo parlor ta xauna tana kallon agogo taga har bakwae da sha biyar, ji tayi kmr ta saka kuka, yanxu ina xata ce ma Mumy ta je, haka tayi ta xama har bakwae da rabi, can ta mike ta dau Bible din ta, taji an kwankwasa kofa, still tayi gabanta na faduwa, kaddai yan gidan ne, karasawa tayi a hankali tana leka window ta ga shi ne tsaye, takalminta ta sa ta bude kofar hade da hade rai ta fito xata wuce ya riko hannunta ya wara ido yace "Wait in raka ki mana, Abbana ne muka hadu a mosque ya aikeni fa" ta kallesa kamar xata yi kuka tace "Toh yanxu ina xan ce ma Mumy naje bayan tun six thirty ya kamata in dawo gida" ya langwabar da kai yace "tell her you went to visit a sick frnd" shiru tayi tana kallonsa can ta girgixa kai a hankali tace "My religion is against lies, we don't tell lies" kasa ce mata komai yayi ya kuma kasa daina kallonta duk sai bai ji ddin amsar ba, can yace "And my religion also! Lying is one of the greatest sin in islam" Wani kallo tayi masa sae kuma tayi dariya tace "amma karya kace inyi a gida yanxu fah!" Kallonta kawai yake duk sai yaji ya tsani kansa hakan da yace mata, "I was only joking, idan nace ki shiga wuta sai ki shiga, religion din ki ya hana karya amma bai hana fita night birthday ba koh?" A bit annoyed yayi maganar hakan yasa tayi shiru tana kallonsa bai kuma kallonta ba ya karasa cikin parlon yayi xamansa ta bi sa da kallo, can ta juya cikin sanyin murya tace "Ohk, good nyt" a takaice yace "Nyt!" Ta fita daga parlon, ta kusa minti biyar da fita sai kuma ya mike shi ma ya fita, ko alamar ta bai gani a layin ba, yayi jam din gate dinsa ya bi ta da sauri, yana shan kwana ya hango ta tsaye ta rakube jikin wani flower ya daga k'afa ya karasa gun da sauri, k'arnuka biyu ya gani a gun suna xaune shine yasa ta kasa wucewa, dafata yayi ta fasa wani ihu a tsorace ya juyo da ita da sauri ta fado kansa ya rungumeta, lamo tayi jikinsa yana jin yanda kirjinta ke bugawa kamar xai fito, a hankali tace "Doctor!" Yace "Yes matsoraciya" janyeta yayi jikinsa ya rike hannunta suka ci gaba da tafiya har suka wuce gun karnukan tana shishshige masa, bbu wanda yace komai cikinsu har suka iso bakin gate din gidan nasu ya sake hannunta ta kallesa cikin sanyin murya tace "Thank you" murmushi yayi ya rungume hannayensa yana gyada mata kai, ta mayar masa da murmushin ta bude gate dinsu ta shiga ta daga masa hannu snn ta rufe gate din, lumshe ido yyi ya bude sannan ya juya ya bar wajen. Samantha na shiga gida suka kusa cin karo da Mum dinta bakin kofa, uwar ta hade rai tace "Where are you coming?" Shiru Samantha tayi tana kallonta a tsorace, "Baxa ki bude baki ki min magana ba kina kallona, karfe shidda aka tashi church, daga ina kike yanxu?" Sauke kanta tayi kasa, ta mata wani tsawa tace "Ba kya ji na ne?" Kamar xata yi kuka tace "Am sorry Mum, baxan kara ba" Mum din ta daure fuska tace "Wato ba daga church din ma kike ba ko....." Dad din Samantha ne ya karaso bakin kofar Samantha ta kamo hannunsa hawaye cike idonta tace "Abba kace ma Mumy tayi hakuri baxan kara ba, am so sorry" patting din shoulders dinta Abban yayi yace "It's ohk love kar ki sake dadewa church da an tashi ki dawo gida" kai ta gyada masa, ya ja hannunta suka bar wajen. Karfe tara Samantha na shirin kwanciya Mumy ta shigo tace "Oya tashi ki shirya mu je vigil tunda gobe friday da wuri xaki dawo sch sai kiyi bacci" Samantha tace "Mumy but karatu nake son xan....." "C'mon my frnd tashi kiyi abinda nace, karatu ya fi addinin ki ne" mikewa Samantha tayi bata kuma cewa komai ba ta fara shiri uwar ta juya ta fita, sai da suka yi ma Dad sallama snn driver ya fita da su xuwa church a mota, suna kusa kai wa dai dai gidansu Abuturrab Samantha ta hango gate din a bude sai gashi ya fito da mota, dai dai tsakar titin ya bude motar ya fita ya shiga gida don kulle gate din, masifa Mumy ta shiga yi Driver na taya ta don ya tare masu hanyar wucewa, Abuturrab ya fito da niyar xai basu hakuri Mumy ta sauke glass cike da masifa tace "Kai halan titin nan na Ubanka ne?" shiru yayi yana kallonta don sarai ya ganeta, Samantha sai kallonsa take, can ta kamo hannun Mumy tace "Mumy kiyi hakuri kila bai san...." Turata uwar tayi tace "Uwarki, shi makaho ne bai hango motar mu ba?" Abuturrab ya dauke kai ya nufi motarsa ya bude ya shiga ya gyara parking ya basu hanya, har suka wuce idonsa na kan motar. Ranan Juma'ah yana isa main road xai je masallaci ya hangota tana saukowa daga motar gidansu, tana sauka kuma motar ya wuce, xata wuce motarsa yace "Hello!" Juyowa tayi da sauri tana ganinsa tayi murmushi ta d'aga masa hannu. 📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 5..... Ganin yaki tafiya ta karasa kusa da motar tace "Ina yini?" Yace "Lafiya ya schl?" Kai kawae ta gyada masa yace "baki yi bacci bane see ur eyes!" Langwabar da kai tayi tace "We went for vigil" ya kalli wrist watch din hannunsa yace "Come in let me drop you" ta xaro ido tace "Ba masallaci xaka je ba?" Yace "There is still time" xagawa tayi ta bude front seat ta shiga, yayi reverse ya juya, a hankali tace "Sorry for what happened yesterday night" murmushi yayi yace "Yeah am at fault, gaskiya mama ta fadi" bata kuma cewa komai ba har suka iso bakin gate dinsu yayi parking ta bude motar ta fita ta rufe snn ta jingina jiki tace "Thank you" gyada mata kai yayi tace "Don't forget to pray for me fa" murmushi yayi yace "Alryt," daga haka ta nufi gate shi kuma ya tada motar ya bar layin. Washegari da ya kasance asabar Abuturrab na dawowa daga masallaci ya shiga main house don gaida Abba kasanacewar yana gari, Abba ya amsa gaisuwarsa idonsa dake dauke da glass a kan laptop din dake gabansa, can Abuturrab ya mike da nufin wucewa Abba yace "Ina fa da magana da kai Ali" komawa yayi ya xauna yace "Toh gani Abba" Abba bai ce komai ba har na kusan minti biyar sai kuma yace "How about planing of settling down Aliyu!" Shiru Abuturrab yayi don sai da gabansa ya fadi, Abba yace "Yes it's high time you do that, you will be thirty one soon...." Abuturrab ya sauke kansa kasa kana yace "Abba komai fa lokaci...." Abba ya dakatar da shi ta hanyar cewa "Don't tell me that, Sai yaushe lokacin xai xo?" Shiru yyi bai ce komai ba, Abba yace "Go and think about it pls" a hankali yace "Toh Abba nagode" daga haka ya mike yyi masa sallama ya fita, bedroom din Maminsa ya nufa ya sameta xaune har lkcn kan darduma, Khaleesat kuma na kwance kan gado tana bacci, ya xauna bakin gadon, can ya gaji da xaman yayi kwanciyarsa kawae, sai kusan bakwae Mami ta gama Azkar dinta ta mike ta dauke darduman tana kallonsa don idonsa a lumshe yake tace "Abuu are you sleeping?" Bude idon yayi ya mike xaune sannan ya sauko kasa ya gaisheta ta amsa tace "Ka tashi lafiya?" Yace "Yea, but Abba spoilt everything" Mami ta d'an bude ido tace "Me kuma ya faru" ya marairaice yace "Mami wai maganan aure fa Abba ke min, yaushe ma na girman" Mami tayi murmushi tace "Mancewa kayi, jiya ka girma" yace "Allah Mami kije kiyi masa magana kice ur son is not grown up yet, yaushe ma kika daina ban madara da daddare?" Dariya Mami tayi ta xauna gefen gado tace "Silly you! c'mon tashi ka ban waje, it's better kaje ka xauna ka yi tunani da kyau kaga what's good for you, kilan idan kayi aure zaka nutsu" mikewa yayi yace "Am not ready for marriage Mami, toh waye xai xama mijin ma idan aka yi auren... Ita ko ni" Bai jira cewarta ba ya fice ta bi sa da kallo tana murmushi, jallabiyar jikinsa ya cire ya dau kayan sport dinsa ya sa ya dau chill Coke a fridge snn ya fito ya nufi gun da yasa aka tula masa kayan gym, ya kusa awa daya gun yaji kamar an bude gate, xagayowa yayi da sauri, tsaye tayi bakin kofar tana kallonsa hannunta rike da littattafai tana sanye da bakar abaya tayi rolling kanta, ganin kallon da yake mata yasa ta kasa tsaye gu daya, can tace "Um Good morning" sai kuma ta juya da sauri xata wuce, yace "Frnd!" Juyowa tayi, ya mata murmushi ya karasa kusa da ita ya rungume hannayensa yana kallonta, sunkuyar da kai tayi, yace "Ina xa ki this early morning?" Dago kai tayi ta kallesa tace "Lesson, waec lesson!" Yace "Ohh that's nyc, how was ur nyt?" Ta wara ido tace "Splendid! Xaka min assignment plss sir" langwabar da kai yayi yace "Assignment kuma, which?" Tana kkrin bude littafin tace "Physics and Biology" mika masa tayi ya karba yana kallo snn yace "Uhm!" Tace "You are busy koh?" Ya kalleta yace "Sai yamma zan fita aiki, am around now" cike da shagwaba tace "Toh ka min plss" kallonta kawai yake, can yayi murmushi yace "Ohk, but I will only show you how to solve it, and you do the rest by ur self" ta xaro ido tace "But am going to lesson...." Yace "Wannan ma ai lesson ne" shiru tayi tana kallonsa, ya mika mata littafin yace "Shiga ki ajiye a ciki, tare xa muyi" a hankali ta sa hannu ta karba littafin ta nufi cikin parlon amma da gani ranta bai so ba, ya sauke hannunsa ya bi ta da kallo sai kuma ya juya ya koma gun gym din ya dau sauran coke dinsa ya shiga parlor, tsaye ya ganta ya karashe shanye coke din ya wurga can din yace "Why standing like a soldier?" Murmushi tayi ta d'an dosana kugunta jikin kujera, ya karasa parlon yace "Let me freshen up sai mu fara" kai ta gyada masa kawai ya dau hanyar bedroom dai dai lkcn da aka danna bell, dawowa yayi da sauri ita kuma ta mike tana kallonsa da damuwa tace "ur sisters koh" bai tanka ta ba ya nufi kofar ya leka ya ga peter ne dauke da breakfast, bude kofar yayi ya karba ba tare da ya amsa gaisuwar da yake masa ba yace "Thank you" sannan ya rufe kofar ya karasa parlon ya ajiye, har lkcn tana tsaye tace "Kar sisters dinka su xo fa" yace "Bbu kowa gidan fa, duk sun tafi islamiyya" a hankali ta koma ta xauna, ya wara mata ido snn ya wuce, ya kusa minti talatin kafin ya fito sanye da farin polo da 3qtr baki ya shigo parlon yace "Sorry for keeping you waiting" murmushi kawai tayi ya xauna kan rug ya matso da tray din breakfast din da aka kawo mai, ya kalleta yace "Je kitchen ki kawo wani cup plss" ba musu ta mike ta wuce kitchen din sai ga ta ta dawo da cup ta samesa yana hada tea me kauri, ta ajiye masa cup din ta koma ta xauna, ya hada wani snn ya kalleta yace "Taho muyi breakfast" ta xaro ido tace "Noo, ni fa na k'arya" gyada kai yayi yace "Ashe ko baxa ayi assignment din ba yarinya" ta marairaice tace "Da gaske fa doctor na ci abinci" ya hade rai sosai yace "Toh ai shknn" shiru tayi tana kallonsa sai kuma ta mike ta karaso kamar xata yi kuka ta xauna, yace "Allah ya taimake ki da bbu abinda xan maki" murmushi tayi ta sunkuyar da kai, ya ajiye mata cup din tea a gabanta, snn ya debi potatoe, yam, egg, plantain a plate daya ya ajiye mata sai pepper soup din naman ram ya ajiye mata, ta marairaice tace "baxan iya cinye su ba Dr" yace "Ohk to mu ci tare" dawowa yayi gefenta ya xauna ta kallesa ta gefen ido, ya dau fork daya ya ajiye mata daya snn ya soma ci, da kyar ta iya daukar fork din don duk a takure take ta dauki potatoe ta kai baki a hankali tana satan kallonsa, sai cin abunsa yake, ganin yanda take tsakuran abincin ya ajiye fork din hannunsa yana facing dinta yace "Kinsan Allah idan baki ci abincin nn ba bbu abinda xan maki" ta xaro ido tace "Kaga ina ci fahhh" hararanta yayi ya ci gaba cin abunsa, haka yasa ta bude ciki ta ci abincin sosai don sai da suka cinye wanda ya diba snn ya shanye tea dinsa ya mike yace "Fast ki shanye tea din mu fara" kai kawai ta gyada masa kamar xata yi kuka don ta koshi. Yana kallo ta dawo kusa da shi daga kasa ta xauna tace "Doctor na gama" kallon wajen yyi ya ga wayam ta kwashe komai yace "Are you sure kin shanye shayin kuwa" ta turo baki tace "In kawo cup din ka ga?" Ya gyada kai yace "Alryt! Kwaso books din" mikewa tayi, tayi yanda yace ta ajiye su a kasa, ya sauko ya rage volume din Tv din, ya bude physics book din yana kallo, shafa beard dinsa yayi ya lumshe ido ya bude yace "Ohk, listen attentively" tace "Toh" a nutse ya shiga mata solving din questions din yana mata bayani, ya maimaita ya kai sau biyar har sai da tace ta gane, yayi forming questions uku ya bata tayi ta karba tana kallo, ya mayar da hankalinsa kan kallon da yake, tana gamawa ta kallesa tace "Am through" karba yyi yana dubawa, can ya gyada kai yace "Then do ur assignment now" tace "Toh" snn ta fara assignment din, ko da ta gama tare suke yi biology din har suka gama, ta kalli agogo taga goma ya kusa ta kallesa kafin tace komai yace "Lokaci ya riga ya wuce, just read ur note...." Xaro ido tayi tana kallonsa tace "Ohk to xan tafi gida" yace "Mum xata tambayeki why you came back early" shiru tayi bata ce komai ba, yace "So it's better ki jira time yyi sai ki wuce" ita dai bata ce komai ba, yyi kwanciyarsa kan 3 sitter ya canxa station, wani American film ake yi tayi tagumi ita ma tana kallon movie din, gajiya tayi ta bude essential bio dinta tana kallo, kmr ance ta dago kai ta kalli Tv abinda ta gani yasa ta kallesa da sauri, lumshe ya ga idonsa, bata kuma kallon Tvn ba ta mike da sauri tayi hanyar kitchen, plates din da suka yi breakfast ta shiga wankewa tana gamawa ta gyara kitchen din snn ta fito da sweeper da mop har lkcn rufe ta ga idonsa sai ta ga kamar bacci ma yake, gyaran parlon ta fara yi da yake bbu wani kura cikin few minutes ta gama gyaran ta mayar da komai inda yake ta dawo ta kalli agogo ta ga sha daya ya kusa, one sitter ta xauna ta canxa station xuwa Bollywood, bata yi minti goma tana kallon ba ta jinginar da kanta jikin kujera sai bacci, bude ido Abuturrab yayi ta dalilin wayarsa da ya ji yana ring a bedroom ya mike xaune yana kallonta ganin yanda ta takure kan kujeran tana bacci, mikewa yayi ya karasa kusa da ita ya durkusa, long lashes dinta kawai yake kallo ko kiftawa bbu can ya sauka idonsa kan dogon hancinta kafin d'an karamin bakinta, hannunsa ya daura kan fingers dinta ta bude ido da sauri, ya mike yace "You are not comfortable xo ki kwanta a can" xata yi magana ya kama hannunta ta mike ya nufi kan kujeran da ya tashi daga yasa ta kwanta snn ya wuce bedroom, missed call din Abokinsa Mujaheed ya gani ya shiga kiransa back, bugu uku Jaheed ya daga, daga daya bangaren yace "Ina ka shiga man?" Abuturrab yace "Was having a Nap at the parlor, ya aka yi?" Jaheed yace "Alryt gani tahowa....." Da sauri Abuturrab ya katse sa ta hanyar cewa "Yanxu fa xan fito office ku hadu a can" Jaheed yace "It's urgent....." Abuturrab ya kalli agogo yace "Ni na ma shirya fa, fitowa kawai xan yi" Jaheed ya d'an yi tsaki ya katse wayar, Tabe baki Abuturrab yayi xai shiga toilet ya ji ana danna bell, fitowa yayi da sauri, ga mamakinsa ko motsi Samantha bata yi ba, baccinta kawai take, kofa ya nufa a leka waje yaga Mami tsaye, xaro ido yyi ya juya da sauri ya isa gun Samantha tashinta ya shiga yi ta bude ido a hankali tana kallonsa, sai kuma ta mike xaune tana kalle kalle dai dai lkcn da Mami ta kuma danne bell tace "Abuu?" Mikewa Samantha tayi a tsorace tana kallonsa da kyar tace "Ur Mum?" Bai ce komai ba ya kama hannunta ya wuce bedroom dinsa da ita tana shiga ya rufe kofar snn ya fito ya koma gun Kofar ya bude, sai ka rantse daga bacci ya tashi yanda yyi da fuska, Mami tace "Bacci kake?" Gyada Kai kawai yayi, tace "Ohk sorry, ka xo ku gaisa da Yakumbo ta xo" shiru yyi yana kallonta sai kuma ya hade rai yace "Mami maimakon kice na fita aiki?" Mami tace "Go and freshen up ka fito ku gaisa nace, bana son magana" daga haka ta juya ta bar gun tana kallon karen dake cage abinsa, girgixa kai tayi tayi gaba. Abuturrab yayi tsaki ya juya ya koma bedroom dinsa, durkushe ya ganta bakin kofa ya buda ido yace "Me kike a nan kuma?" Kallonsa tayi bata ce komai ba, yayi murmushi ya nuna mata gefen gado yace "Kiyi xaman ki, or are you afraid, she's gone already?" Mikewa tsaye tayi ta girgixa kai tace "A'a xan wuce gida karfe sha biyu muke dawowa daga lesson din" kallon agogo yayi sai kuma yace "Alryt, me xaki yi a gida yanxu idan kika koma?" Tace "Idan Mumy bata nan xan yi girki, that's all, da yamma kuma in tafi catechism" ya rungume hannayensa yace "Uhn ashe kin iya girki" xaro ido tayi tace "Kai!" Sai kuma tayi murmushi ta dauke kai, yace "Ohk idan ke kika yi girkin ki xubo min xan ci" ta kallesa da sauri tace "Da gaske?" Ya gyada mata Kai, tace "Ohk xan kawo maka" daga haka ta juya tace "Bye na tafi" yace "in raka ki?" Girgixa Kai tayi tace "Noo, thank very much" daga masa hannu tayi ya bi ta da ido har ta fita daga dakin, murmushi yayi ya sauke hannayensa ya shiga toilet, wanka ya kuma yi ya fito ya shirya cikin kananun kaya ya fito xuwa main House, da sallama ya shiga parlon, Yakumbo dake xaune tare da Mami ta bi sa da ido har ya karaso parlon, xaunawa yayi a kasan lallausan carpet din dake malale tsakar parlon ya gaisheta, ta tabe baki tace "Lafiya lau, ya aiki?" Ya shafa kai yace "Alhmdllh" Tace "Wato dai har gobe baxa kayi xumunci ba ko Aliyu, nan nan yayanka ya dawo daga Germany bayan shekaru masu yawa amma ka kasa xuwa inda yake ka gaishesa" Abuturrab ya d'an hade rai yace "Umma na kirasa fa...." Tace "Rufen baki, kira nace ko xuwa can" dauke kai yyi, Mami dai bata ce komai ba, Yakumbo tace "Ba dai ka da kamarsu a duniya wllh, idan ka so ka rike su da mutunci su ne iyayenka gobe" Mikewa Abuturrab yayi ya nufi kofa, ta bude baki tace "Ohh ga shegiya na magana koh?" Ko juyowa bai yi ba har ya fice, ta kalli Mami tace "Hajarah anya tarbiyar arxiki kika ma Aliyu kuwa, yo ashe idan Ahmad na masa magana xai iya tashi ya wuce" Mami bata ce komai ba ta mike ta bi bayansa, har ya kusa part dinsa ta gansa tace "Aliyu" juyowa yayi yana kallonta ta karasa tace "Are you stupid ake maka magana xaka tashi ka wuce" yace "Haba Mami ni me yasa matar nn baxata kyaleni bane a rayuwar nn, komai nayi tace bai yi ba, ni gaskiya darajar Abba yasa nake daga mata kafa....." Tsawa Mami tayi masa tace "Koma dai meye yayar Mahaifin ka ce, and you have to respect her the way you will respect ur father...." Bai kuma cewa komai ba ya dauke Kai, tace "Maxa ka koma ka bata hakuri kar in saba maka" da kyar yace "Ohk Mami, amma sallah xanje yi masallaci yanxu" bata ce komai ba ya nufi gate, ta girgixa Kai ta juya ta koma gidan, ko da Abuturrab ya dawo daga masallaci sai da ya ga dama ya shiga gidan bbu yabo bbu fallasa ya bata hakuri ya fice daga parlon, karfe hudu yana shirin fita gun aiki aka danna bell a parlor. Haske writers asso📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 6..... Fitowa yyi ya bude kofar parlon ya ganta tsaye rike da basket din abinci, wara ido yayi yana kallonta, tace "Um na kawo maka abincin" rungume hannayensa yayi yana murmushi yace "Da gaske?" Ta gyada masa kai ya bata hanya ta shiga parlon ya juya ya bi bayanta, tsakar parlon ta ajiye abincin ta kallesa ya sakar mata murmushi yace "Thanks Samha!" Mikewa tayi ta dau jakarta tace "Uhm am going to church!" Shiru yayi yana kallonta, ta wara masa ido tace "Bye" daga haka ta nufi kofa ya bi ta da kallo, can ya bi bayanta da sauri yace "Church kuma?" Ta kallesa tace "Eh Catechism xan je" rasa abinda zai ce mata yyi, ganin har ta fita ya bi ta yace "Which means baxa ki rakani ba knn, ke fa nake jira....." Ta juya tace "Ina xan rakaka?" Ya langwabar da kai yace "Clinic xan je duba patients dina" tayi shiru tana kallonsa, can tace "Toh church din fa, it's being a long time bn je church ba fa" yace "Ehh to daga can sai inyi dropping din ki a church din" bai jira cewarta ba ya juya ya dau car key a daki ya dawo yace "Mu je" yana gaba tana biye da shi suka isa gun motarsa ya bude mata snn ya tafi ya bude gate yana fita da motar ya fito ya rufe gate din snn ya shiga ya dau hanyar Clinic din da yake aiki, Ba tare da ya kalleta ba yace "Tell me about ur self!" Ta d'an kallesa sai kuma tayi murmushi tace "Ohk" jinginar da kanta tayi jikin kujera a hankali tace "Sunana Samantha David, but my baptism name is Rebecca, I am an only child, ni kadai parent dina suka haifa, I was born and brought up into a devoted Christian home, My maternal grandfather is a pastor, and my Mum Rachael took over him my mum is a Ghanian....." Shiru tayi tana kallonsa, duk da ba kallonta yake ba idonsa na kan titi amma gaba daya hankalinsa na kan abinda take cewa, still ba tare da ya kalleta ba yace "Ur Dad?" Ta wara ido tace "Sunan Abbana Aliyu Umar, but he's baptism name is David, my paternal grandfather is a Muslim, a Fulani from Adamawa, he married my paternal grand mum that was a Christian after he converted her to Islam, my father was the 1st child daga shi sai kanninsa mata biyu, duk suna kanana babansu ya rasu, shine Mum dinsu ta daukesu ta koma Ghana sbda akwai yayanta Christian a can, and that was where she re- converted to Christianity, then Abbana was still practicing the Islamic religion but when he met my mum at Sikkim Manipal University SMU sai ya koma Christian shi ma, buy he's younger sis Khadija is still a muslim she's in kaduna....." Driving kawae Abuturrab yake amma da ganin yanayinsa kasan takaici ne karara a tattare da shi, Ta langwabar da kai tace "My dad is a politician, he's a true devoted Christian also like my Mum...." Gyada kai yayi don bai ma son ci gaban labarin yace "That's nyc...." ta kallesa tace "Toh ni baka fadi min about ur self ba" shiru yayi na d'an lkcin kafin yace "Am Aliyu Ahmad, an only son with three siblings, My mum was a lecturer then, My dad a soldier.... I think that's all" Kallonsa kawai take ya kure wakar da ke tashi a motar don bai son magana kuma, har ya isa asibiti bbu wanda yace komai, yana gama parking ya kalleta ya bude motar ya fito ita ma ta fito tana kare ma asibitin kallo, tana biye da shi a baya suka shige reception, nurses din sai gaishesa suke sai dai ya gyada masu kai, ita kuma su bi ta da kallo har suka haura sama ya bude office dinsa, sai da yasa ta fara shiga snn shi ma ya shiga ya bude curtains ya kunna A.c ya xauna, tana kallonsa a hankali tace "I will like to be a doctor like you also" d'an murmushi yayi ya mike ya nufi fridge ya fiddo coke biyu ya mika mata daya ta karba ya bude dayan ya fara sha, kallonsa kawai take ko kiftawa bbu, ji tayi komai yayi burgeta yake, bai ajiye can din ba sai da ya shanye ya juya yana kallonta yace "If you study hard you will be a medical doctor also" wara ido tayi tace "Ohk I will by the grace of God" Wani d'an wardrobe ya nufa ya bude ya fito da pure white laboratory Coat dinsa ya saka ya dau stethoscope ya nufi kofa yace "taso mu je mu duba patients dina" mikewa tayi ta bi bayansa suka fita, haka ya dinga bin ward ward tana biye da shi duk jikinta a sanyaye ganin marasu lafiya abun tausayi a kwance, second to the last ward din da ya shiga ya juya bayan ya gama duba patients din ciki ya ga bbu ita, juyawa yyi da sauri ya fita ya ganta durkushe jikin bango hawaye a idonta, da mamaki yace "What happened?" Ta fashe da kuka ta mike tace "Doctor bana son gani kuma....." Rungume hannayensa yayi ya bude ido yace "is that why you are crying?" Bata ce komai ba sai hawaye, yyi murmushi yace "Alryt, tafi office ki jira ni" ba musu ta dau hanyar office din ya bi ta da kallo. Ko da ya koma office xaune ya ganta ta kife kanta da table, ya karasa yana kallonta ya duka gabanta, bak'in gashin kanta dake kyalli yake kallo ta dalilin xamewa da dankwalin kanta yyi, a hankali ya sa hannu ya karasa xame dankwalin don a rayuwar sa bbu abinda yake so kamar yaga gashin kan mace da tsayi, sai da ya rike breathe ganin gashinta din dogo ne ba na wasa ba ga tsantsi ga baki, kana ganinta kasan ta hada jini da Fulani, hannu ya daura a Hankali kan gashin yaji uban laushinsa, bude ido tayi ya koma baya da sauri ta mike xaune tana kallonsa tace "Doctor" wara ido yayi ya fara kame kame yace "Oh! you've... You've got a beautiful hair..... It's... It's very fine" mayar da dankwalin kanta tayi bata ce komai ba ya mike yana shafa kansa yace "har na gama duba patients din...." tace "Toh xan wuce church" kallon agogo yayi yaga biyar ya gota yace "Ohk...." Bude kofar office din aka yi, wani guy da baxai wuce Abuturrab ba ya shigo yace "Kai fa dan rainin wayo ne Aliyu, ina ta jiran....." Shiru yayi ganin Samantha, barin da ya ganta xaune kan office chair, Abuturrab yace "Yanxu fa da xan kira ka, to muje in ji urgent call din...." Daga haka ya nufi kofa, Jaheed dake ta kallon Samantha yace "Bakuwa kayi ne?" Abuturrab yace "Yea!" Snn ya fita, Mujaheed ya kalleta kafin yace komai tace "Ina yini" yyi murmushi yace "Lafiya lau, ykk" ta sunkuyar da kai tace "Lafiya lau" juyawa yyi ya fita, ba a wani dau lkci ba Abuturrab ya dawo yace "Ohk let get going" ta mike daga zaunen da take suka fita. Hanyar da yasan xa su hadu da traffic sosai ya bi da su, duk ta damu ita church, ko kallonta bai yi ba har sai da yaga shidda yayi yace "Wai karfe nawa ake tashi daga church din naku ne?" Kamar xata yi kuka tace "Six mana" ya dauke kai yace "Ashe ma an tashi kenan...." Bata kuma kulasa ba amma da gani xaka gane ranta ya baci, bai damu ba har ya isa kofar gidansu yyi parking xata fita ya riko hannunta, juyawa tayi tana kallonsa ya ga hawaye idonta, da mamaki yace "Kuka kuma?" Share idon tayi bata ce komai ba, yace "Toh Allah baki hakuri, but you can still go the church...." bata ce komai ba ta bude motar ta fita bai yi wata wata ba ya ja motarsa yyi reverse ya nufi gida ta bi motar da kallo, a sanyaye ta bude gate dinsu ta shiga. Abuturrab na dawowa daga masallaci ya bude abincin da ta kawo masa, Shinkafa ce da miya sai fried cow meat a wani gun daban da kayan vegetables da aka yanka, kallon abincin kawai yake duk da ya burgesa a ido amma bai jin xai iya ci, ya tabe baki ya mike ya dau naman ya kai ma karensa da ya fara sabawa da ya ajiye masa a cage, abincin kuma ya dauka ya kai ma masu gadi ya dawo ya xuba abincin da Ramla ta kawo masa ya ci kadan ya tafi masallaci, yana dawowa ya ganta da Mum dinta suna tahowa da kafa ko ina xa su, ido hudu suka yi da Mum din tata, tayi masa wani matsiyacin kallo da alamar ta tuno tare masu titi da yyi ranan ne, haka kawai yaji gabansa ya fadi, ya dauke kai ya ci gaba da tafiyarsa, Samantha sai kallonsa take har ya shiga gate. Washegari Sunday throughout bai ganta ba har yamma, duk sai yaji bbu dadi ganin har karfe shidda bai ganta ba, mikewa yyi daga karshe ya fita ya dau hanyar gidansu kamar me strolling har ya gama tafiyarsa bai ganta ba ya juya kawai ya dawo gida, har ranan laraba Abuturrab bai hadu da Samantha ba duk yaji sa bbu ddi har abun ya dinga basa mamaki, wai d'an sabon nn da suka yi har xai damu don bai ganta ba, yana xaune parlor tare da su Mami da yammacin ranan alhamis, Mami tace "Abuu!" D'agowa yyi da Sauri yana kallonta, tace "What's wrong with you?" Buda ido yyi yace "Nothing Mami...." Ta girgixa kai tace "Noo, ni fa na haifeka daga jiya xuwa yau naga you are not ur self....." Khaleesat tace "Mami baki yi noticing da kyau ba, for the past two weeks yanxu ya Turab ya canxa, he no longer talk to us, idan ma muka je part dinsa koran mu yake, he no longer treat us well...." Ilham tace "And he's alwayz closing his door don ma kar mu shiga" Ramlah tace "I think his dog is now his everything...." Abuturrab dai sai bin su da kallo yake, Khaleesat tace "or may be yana jin haushin Abba ya maida sa BQ ne, but it's not too late ya Abuu you can still beg him ya bar ka ka dawo nan" Abuturrab ya tabe baki ya ci gaba da kallonsa, Mami tace "Aliyu!" Kallonta yayi tace "Meye matsalar ka?" Ya girgixa kai yace "Bbu komai Mami, am just occupied with work ne yanxu" Mami tace "Toh shknn Allah ya mana jagora..." Mikewa yyi yana kallon khaleesat yace "Ke kuma kika sake ce min Turab sai na gurje bakin ki" daga haka ya kalli wayarsa dake ring yace "Jaheed ya xo Mami... Later xa mu shigo" Mami tace "Ohk Allah ya kai mu" daga haka ya fita xuwa bangaren sa Khaleesat ta bi sa da harara, Xaune ya ga Mujaheed yana ta kallon k'aren dake xaune cage, Abuturrab yace "Welcome!" Mujaheed ya mike yace "Yanxu pls meye ma'anar Dog din nn maimakon mai gadi" Abuturrab ya wara ido yace "Ya fi su iya gadi...." Mujaheed yayi dariya daga haka suka shiga parlor, Abuturrab ya dauko masu can coke a fridge, Jaheed yace "Kaga maganan serious nake son muyi Man kada kuma ka raina min hankali" Abuturrab bai ce komai ba sai da ya ajiye empty can din coke din hannunsa snn yace "Ina jin ka" Jaheed yace "Old man dina ne ya takura ni maganan aure this dayz wllh, am just confused donno what to do..." Abuturrab ya buda ido sai kuma yyi murmushi yace "Salima fah?" Harara Jaheed ya watsa masa yace "Salima har macen aure ce?" Abuturrab ya d'aga kafada yace "Ohk, nima of recent Dad dina ke min xancen aure...." Jaheed yace "Ae gwara kai kana da Saudat" Shiru Abuturrab yayi, Jaheed ya shafa kai yace "Gaskiya ka sama min solution, just few months ya ban if not ya hada ni da koma wacece ta xo masa a kai" Abuturrab yyi yar dariya yace "Amma kuma duk yan matan ka Mujaheed" Jaheed yayi tsaki yace "Kaga if you don't have anything good to say in tashi in kara ma motata mai" Abuturrab yayi murmushi yace "Kawai ka fara neman mata yanxu...." Jaheed yace "Wacece wnn yarinyar da ka taho office da ita ranan" wani kallo Abuturrab ke yi masa, wanda hakan Mujaheed yace "Ohk sorry ban san budurwar ka bace" Abuturrab yace "Ba budurwa ta bace" Jaheed yace "Then why the frowning of face?" Abuturrab ya tabe baki, sai kuma yyi murmushi yace "She's a Christian" xato ido Jaheed yyi yace "Christian kuma?" Abuturrab ya gyada Kai, shiru jaheed yyi yana kallonsa, can ya girgixa kai yace "That's sad, amma a ina ka san ta?" Abuturrab yace "Ga gidansu can few houses from ours" Jaheed yace "Lallai, babban magana kenan" Mikewa Abuturrab yayi jin kamar motsi a gate ya fita da sauri jaheed ya bi sa da kallo, bai ga kowa gate din ba da kuma alamar iska ce don a bude Jaheed ya bar sa, juyowa yyi ya koma parlon. Washegari friday Abuturrab na dawowa daga masallaci misalin biyu da rabi ya dau faran kujerar roba ta xauna waje jikin flower yana dannar wayarsa kunnensa sakale da earpiece, tun daga nesa ya hangota tana tahowa, ya kasa dauke idonsa a kanta ko kiftawan kirki bai yi har ta iso inda yake, ga mamakinsa sai ya ga taki kallon gun har ta wuce sa, bai san lkcn da yace frnd ba, ta juyo tana kallonsa. *Haske writers Asso*📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 7...... Sunkuyar da kanta tayi ta dawowa cikin sarkewar murya tace "Ina yini" kallonta kawai yake ganin yanayinta yace "Baki da lafiya ne?" Kin cewa komai tayi kuma taki d'agowa ya mike yace "Talk to me mana, what's wrong?" hawaye ya cika idonta ta gyada masa kai, kalle kallen anguwar yayi, kawai ya kama hannunta suka shiga gida ya kulle gate din, parlor ya nufa da ita bayan yasa ta shiga da takalmanta ya rufe kofar yana kallonta yace "Since when?" xaunawa tayi kan kujera ta kwantar da kanta jiki ya durkusa gabanta yace "ina ke maki ciwo?" Xamowa kasa tayi ta hade kanta da gwiwa ta fashe da kuka bata ce komai ba, jin kukan nata ya dinga yi har xuciyarsa ya dago kanta ya dafa shoulders dinta da damuwa yace "Talk to me mana, ina ke maki ciwo" kalle kalle ta shiga yi can ta mike da sauri ya rikota xai yi magana ta toshe bakinta tana kkrin kwace hannunta, da sauri ya saketa ya mike ya kama hannunta suka nufi toilet dake parlon da ita, amai ta dinga kwararawa yana kallonta har ta gama tana mayar da numfashi ya debo mata ruwa ta wanke bakinta ya gyara wajen ya fito da ita, kwanciya tayi nan tsakiyar parlon tana juye juye, sai kuma ta fashe da kuka, ya hade rai yace "Kinga idan baxa ki min magana ba ki tashi kiyi tafiyar ki, leave now" mikewa tayi da kyar xata fita ba tare da ta kallesa ba ya bi bayanta da sauri ya jawota ta fado jikinsa, rufe fuskarta tayi jikinsa tana kuka a hankali, sun kusa minti uku a haka ya dago kanta a hankali yana kallonta yace "You are on ur period?" Sauke idonta tayi bata ce komai ba sai hawaye, komar da ita yayi ya xaunar kan kujera ya shiga bedroom dinsa, da yake baya rasa magunguna da allurori na Dysmenorrhea sbda kanninsa daukowa kawai yayi ya fito parlor, kwance ya ganta kasa, ya fara hada alluran yana gamawa ya dawo kusa da ita yace "Kin ci abinci koh?" Cikin kuka tace "Na sha tea" yace "Ohk, let me inject you, xa ki samu relief kin ji" bai jira cewarta ba ya fara daga doguwar gown din jikinta, ta rike da sauri don dama ita ba gwanar sa dogon wando bace, muryarta na rawa tace "Doctor ban sa komai ba...." shiru yayi yana kallonta sai kuma ya mike ya shiga daki ya dauko towel dinsa ya fito ya bata yace "to tashi ki daura," ta mike ta karba ya dauke kai ta daga gown din ta daura, kujera ta tafi tayi rub da ciki ta runtse ido ya bi bayanta, a hankali ya sauke towel din yayi mata alluran, yana gamawa ta fashe da kuka ya dagota xuwa jikinsa yace "It's okay xae daina maki yanxu" Kai kawai take gyada masa, sai da yaga ta nutsu snn ya saketa, ta xamo k'asa ta kwanta ta rufe ido, durkusawa yyi yana kallonta, ba a wani dau lkci ba bacci ya dauketa, ya mike yayi disposing syringe da kwalban alluran ya dawo parlon ya taimaka mata ta koma kan kujera. Yana bedroom aka danna bell ya fito da sauri ya nufi kofar, ganin Ramla ce yace "What again?" Tace "Ohh ya Abuu Mami ce fa ta aiko ni ka bude kofar plss...." ya hade rai yace "Pls go am busy yanxu, or you say it out there" murguda baki tayi don bata san yana kallonta ba tace "Ni fa....." Yace "Leave immediately idan ba haka ba xan sa ki kuka if I shud open this door" juyawa tayi fuu ta wuce. Sai kusan karfe shidda Samantha ta tashi daga baccin, yana parlor har lkcn yana danna laptop, ta mike xaune da sauri tana kallon agogo tace "Wayyo my mum is at home...." ya kalleta snn ya kalli agogo ta mike da sauri xata sauke gown dinta ta cire towel dinsa taga towel din yyi stain, still tayi tana kallon wajen, ya mike yace "What" girgixa masa kai tayi ta nufi toilet dake parlon da sauri, ya bi ta da kallo, cire towel din tayi xata wanke taji yace "Don't worry xan wanke....." Kasa juyowa tayi ta girgixa kai tace "No, xan wanke" juyo da ita yyi yace "Nace xan wanke" ta sauke idonta kasa bata ce komai ba, murmushi yayi yace "Yess" ajiye masa tayi ta nufi kofa ta fice daga toilet din sannan ta bar gidan gaba daya, tana isa gida gabanta ya fara faduwa, daga taje chemist a bata Magani tun uku saura sai after six take dawowa, mai aikinsu Blessing ce ke ta goge goge parlor, Samantha tayi kasa da murya tace "Mumy fah Blessing?" Blessing tace "Ta fita church tun daxun" Samantha ta sauke ajiyar xuciya tace "Bata tambaye ni ba" Blessing tace "No, tayi tunanin kin sha Magani kin kwanta a daki ne" Samantha bata ce komai ba sai dai tausayin kanta kawai take don kwata kwata Mumynta bata da wani lkcnta sai na church, duk ciwon da xata yi bbu abinda xae sa Mumy tayi fashin church in ma bata tilasta ta a hakan sun je church din tare ba, ga Abbanta ba wani xama yake ba ta dalilin aikinsa. Washegari asabar da safe Mumy ta shirya xa su Kaduna da tawagar pastoci kamar ta, Samantha na bacci ta tada ta tace "Rebecca you take care of ur self plss xan tafi yanxu, idan baxa ki xauna tare da Blessing ba ki tafi gidansu Stella, by the grace of God ran Monday ko Tuesday xa mu dawo, ki tabbatar kina shan maganin ki...." Samantha dake ta murxa ido tace "Toh Mumy Abba yaushe zai dawo?" Mumy tace "I don't know, just take care of ur self and make sure kin je church anjima da yamma da gobe da safe even if you cannot go to lesson" Samantha tace "Ohk, amma ni gidansu Stella xanje, Blessing ta tafi gida kawai" Mumy tace "Ohk better, ki kuma tabbatar kin tafi da wayar ki ni ban ga amfanin wayar nn naki da kike yasarwa a daki ba" Samantha tace "Toh xan je da shi Mumy, ki taho min da abu me ddi kin ji" Mumy ta nufi kofa tace "Ohk, tashi ki yi wanka ki ci abinci ki sha magani" daga haka ta fita, Samantha ta kalli agogo taga karfe takwas yayi, hamma tayi ta mike ta shiga bathroom, wanke baki tayi, tayi wanka snn ta fito ta kimtsa jikinta ta shirya cikin doguwar rigarta 'yar kanti pink colour da flowers din blue, ta fito da plain veil dinta blue colour ta daura a kai, bata wani yi make up ba sai eye pencil da tasa a ido snn ta sauko, tea kawai ta iya sha dan idan tana period bata iya cin abinci, tana xaune parlor tana ta kallo har Blessing ta gama aikinta tace "Blessing xa ki iya tafiya gida sai Monday nima gidansu Stella xan je ynxu" ba a wani dau lkci ba Blessing ta wuce. Samantha ta kashe kayan wutan gidan gaba daya misalin karfe tara ta hada kayanta kala uku ta dau bible dinta da textbooks na karatu da yake saura sati uku su fara Waec, a hannu ta rike wayarta ta fito ta kulle main gidan tayi ma mai gadi sallama ta wuce, tafiya take kamar mai tausayin kasa har ta iso gate din gidansu Abuturrab, har ta wuce ta dawo ganin kamar gate din a bude yake ta leka, ai ko ta gansa xaune yana sanye da singlet da short hannunsa rike da lighted cigarette, ido hudu suka yi ta juya da sauri xata bar wajen ya mike yace "Frnd" bata ko juyo ba, ya wurga taban hannunsa ya fita gate din, Sauri ya ga tana xubawa yace "Uhm not even a good morning frnd?" Tsayawa tayi bata juyo ba, ya rungume hannayensa yace "Hmm ae shikenan...." Juyowa tayi ta masa murmushi tace "Good morning" yafito ta yyi, ta make kafada, yayi shiru yana kallonta, ta langwabar da kai tace "lesson xan je" yace "Ohk" daga haka ya juya ya koma cikin gate, bin sa da kallo tayi a sanyaye can ta bi bayansa, tsaye tayi bakin gate din tana kallonsa tace "Are you angry" ba tare da ya kalleta ba yana tsaye kusa da karensa yace "No!" Shiga gate din tayi ta rufe ta karasa kusa da shi kamar xata yi kuka tace "You are" ya juya yana kallonta yace "Am not" murmushi tayi tace "Am sorry Dr, um naga baka shirya bane" rungume hannayensa yayi yace "Uhm ban shirya ba kamar ya?" Sunkuyar da kai tayi tana murmushi tace "Kila fa baka yi wanka ba...." Murmushin yayi yace "Toh mu je ki min" xaro ido tayi sai kuma ta juya da sauri xata bar wajen ya rikota yace "Ae sai kin min" boye fuskarta tayi a kirjinsa tace "Nooo Doctor lesson xan....." Rufe bakinta yayi ya ja ta suka shiga parlor ya rufe kofar da makulli. *Haske writers asso* 📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 _Happy Belated born day Asmy B Aliyu, age with grace dear sis, Allah ya karo shekaru masu albarka ya nuna mana auren ki mu xo mu sha biki_😘 8..... Kwace hannunta tayi kamar xata yi kuka tace "Doctor...." Yace "Toh in ruwan ki da rashin wanka na?" a hankali tace "Toh yi hakuri...." Murmushi yayi ya juya ya nufi daki ta bi sa da kallo, can ta ajiye jakar hannunta ta xauna tana kallon program din da ake a tv, bayan minti kusan ashirin taji an danna bell, mikewa tayi da sauri tana kallon kofar, ji tayi ance "Ohh ya Abuu me yasa kake kulle kofa ne yanxu, ni dai ka bude min Mami ce ta aiko ni wllh...." Da sauri Samantha ta mike ta shige bedroom dinsa ta tura kofar tayi lamo jiki, kwata kwata bata ji fitowarsa ba sai gyaran muryarsa da taji a bayanta ta juyo da sauri, daure yake da towel a waist, bakin gashin kirjinsa ya kwanta luf luf don ko goge jiki bai yi ba, a rikice ta juya xata bude kofar dakin ya riko hannunta kamar xata yi kuka tace "Doctor ur sister is outside.... Shi yasa na shigo" key ta ga yasa ma kofar ta juyo da sauri tana kallonsa a tsorace, ya wara ido yace "Tell me what you are afraid of?" Girgixa kai tayi da sauri tace "Noo... Nothing" yayi 'yar dariya yace "Why is it that girls always have this negative thought?" Juyawa tayi bata ce komai ba, yayi murmushi ya kamo hannunta yace "Am not a bad person, erase that thought off ur mind immediately" a hankali tace "Ohk!" Ya kama hannunta ya nufi gado da ita ya xaunar da ita gefen gadon, snn ya dau kayansa ya shiga bathroom, ba a dau lkci ba ya fito sanye da kananun kaya ya dau turaren gaban mirror ya feshe jikinsa da shi ya karasa kusa da ita ya feshe ta ita ma, boye fuskarta tayi jikin gado tana murmushi, can ta dago a hankali taga bbu shi a dakin, mikewa tayi tana kare ma dakin kallo, ko ina fes except from the bed that's untidy, murmushi tayi ta bude curtains din room din ta fara gyara gadon, cikin yan mintuna ta gama ta fita xuwa parlor, xaune ta gansa cup din coffee a hannunsa, ta wuce kitchen ta dauko sweeper da mop ta dawo ya bi ta da kallo har ta shiga bedroom, tana fitowa yace "Well done, thank you" tayi murmushi ta kai abubuwan hannunta kitchen ta fito, yace "Come and make a tea for ur self" tace "Nayi breakfast" yace "Nasan kin yi ae, karawa xa kiyi" tace "Noo na koshi sosai" kan kujera ta nufa ta dau jakarta yace "Ina xa ki?" Tace "Lesson!" Yace "Lesson da jakar kaya?" Ta kallesa tace "Aa xan ajiye gidan wasu family frnds dinmu ne, Mumy ta tafi Kaduna, Abba baya nan, ni kadai baxan iya zama a gida ba shine xan je gidansu" Abuturrab ya ajiye Mug din hannunsa yace "Sbda kina tsoron abu xai cinye ki?" Dariya tayi tace "A'a ni bana tsoro kawai bana son in xauna ni kadai ne" yace "Ohk...." Xaunawa tayi kan kujera ta dalilin ciwo da taji cikinta ya fara mata, kamar ko ya sani yace "Kin samu lafiya Yanxu?" Kai kawai ta gyada masa ta jinginar da kanta jikin kujera, ya bude warmer din dake dauke da wainar shinkafa ya debi biyu ya kalleta ya ga kallonsa take, yace "Taho mu ci" a hankali tace "Masa?" Ya gyada mata kai, tace "Sa min guda daya" yace "Sauko mu ci dai" ba musu ta sauko ta dawo kusa da shi ya kara masu guda biyu, ya debi rich vegetable soup din dake wani warmer a waje daban ya fara ci da spoon, dauka tayi ita ma ta fara ci, ganin yanda take ci kamar ana tilastata yace "Bai maki dadi ba ne" girgixa masa kai tayi da sauri tace "Yayi dadi...." Yace "Then me yasa kike haka da fuska" kamar xata yi kuka ta ajiye Masan hannunta ta kwanta gefensa tace "My tummy" sai kuma ta mike ta koma kan kujera ta kwanta, bin ta yayi da kallo ya ajiye spoon din hannunsa yace "Ya fara maki ciwo" kai ta gyada masa lkci daya hawaye ya cika idonta, a hankali yace "Sorry" mikewa yayi ya shiga bedroom sai ga shi ya fito da allura da Magani ya dawo kusa da ita ya shiga hada alluran, yana gamawa ya kalleta yace "Toh juyo in maki sai ki sha Magani" ba musu ta juyo har xata daga gown din sai ta tsaya kuma, kallonsa tayi hawayen da ke makale idonta ya silalo ta juya masa baya tace "Bude min zip din pls" bude zip din yyi a hankali, ta cire hannun gown din don akwai ves jikinta, ta sauke gown din kasa yanda xai iya yi mata alluran snn ta juya masa baya ta kwanta, daukar syringe din yayi ya mata alluran ta juyo tana kallonsa hawaye na sauka idonta, yace "Sorry!" Ya mike ya dauko table wata ya bata maganin ta sha snn ta koma ta kwanta, bayan awa daya ya kalleta ya ga idonta biyu, yace "Ya daina" ta gyada masa kai, har bayan azahar tana gidan a kwance, yana dawowa daga masallaci bayan anyi la'asar ya durkusa kusa da ita yace "Baki ci abincin ba har ynxu" ta girgixa kai tace "Baxan ci ba" mikewa yayi ya shiga daki ya shirya ya fito da makullin mota yana kallonta yace "Xan je clinic in dawo yanxun..." Mikewa tayi tace "Gida nima xan je" ya hade rai yace "Noo kiyi kwanciyar ki kina tashi cikin xae fara, don't worry i will lock the door" daga haka ya mike ta bi sa da kallo har ya fita, har shidda bai dawo ba, ta sauko da kyar jin cikin xae fara mata ciwo ta xuba abincin da aka kawo masa daxu ta ci kadan ta dau sauran magungunan da ya bata ta sha ts koma ta kwanta, tana kwanciya bacci ya dauketa.. A hankali ya durkusa kusa da ita yana kallonta ganin tun da ya dawo take bacci, can ya kalli agogo ya dafata yace "Frnd!" Da gani kasan bacci me nauyi take da kyar ta bude idonta, yace "Cikin ya daina" ta gyada masa kai a hankali hade da lumshe ido, dagota yayi yace "Taso ki kwanta a ciki, there might be mosquitoes here" girgixa kai tayi cikin sanyin murya irin ta mai bacci tace "A'a gida xan tafi" bai kulata ba ya dagata ta rike sa ta dalilin jiri da taji, ya ja ta xuwa bedroom dinsa, tace "Noo Doctor I want to go home...." Kwantar da ita yyi kan gadonsa ya dau lallausan duvet ya rufa mata ya kai bakinsa kunnenta yace "Go to sleep" rufe ido tayi ya gyara mata gashin kanta a hankali yace "Sleep tight Sam~ha" mikewa yayi ya kashe mata fitilan dakin ya bar na bed side snn ya dau wani duvet din ya fita parlor don idan yace xai shiga wani dakin ma tare da k'ura xa su kwana, kashe wutan parlon yyi ya kwanta kan 3 seater ya lulluba da duvet hade da lumshe ido, ya dade bacci bai daukesa ba, daga karshe dai baccin yayi awon gaba da shi bai tashi farkawa ba sai ana kiran assalatu, mikewa xaune yyi bayan yyi adduar tashi daga bacci ya kusa minti ashirin a haka kafin ya mike ya shiga toilet ya dauro alwala, raka'atainul fajr yyi yana ta xaune kan darduma har yaji xa a tada sllh a masallaci snn ya mike ya fita ya kullo kofar ta waje, ko da ya dawo durkushe ya ganta kusa da gado idonta lumshe ta hade tafin hannunta alamar addu'a take, ya jingina jikin kofa yana kallonta cike da tausayi har dai ta gama, tana ganinsa tayi murmushi cikin sanyin murya tace "Good morning Doctor" ya mayar mata da murmushin yace "Morning how's ur health?" Ta gyada masa kai tace "Na ji sauki yanxu" mikewa tayi ta fara gyaran gado, ya shiga bathroom sai ga shi ya fito da toothpaste da new toothbrush ya ajiye mata gaban mirror ta kallesa tace "Thank you" murmushi kawai yyi ya fita, main house ya nufa don xuwa gaida Mami, a kitchen ya sameta tana hada ma Abba breakfast ya gaisheta ta amsa tace "How was ur nyt!" Yace "Alhmdllh, mene yasa su Ramla ba su yi girkin ba" tace "Na ma gama, he's travelling ne shi yasa...." Abuturrab yace "To where?" Tace "Shiga ka tambaye shi mana" juyawa yayi ya fita ya wuce part din Abbansa, yana kkrin rufe briefcase dinsa ya shigo, Abba yace "How you?" Xaunawa yyi kasa yace "Alhmdllh tafiya xa kayi Abba?" Abba yace "In shaa Allah, ya maganar da muka yi da kai ranan?" Shiru Abuturrab yyi, lkci daya jikinsa yayi sanyi, Abba yace "This is not a matter of u looking at me that way, Yakumbo tace hada bikin da na Yusuf xa ayi..." Kamar xai yi kuka yace "Abba ni fa bani da kowa" Abba yace "That's not a problem, sai ka fara nema yanxu don ina jin nn da watanni biyar ne bikin Yusuf din, idan kuma ka amince mu yi maka xabi it's okay my Stubborn!" Abuturrab bai ce komai ba, Mami ta shigo da sallama rike da tray din breakfast, mikewa Abuturrab yyi ya sallami Abban nasa ya fice, ji yyi ransa ya baci, bai ko kalli Khaleesat dake gaishesa a parlor ba ya fice ya koma bangaren sa ya kusa minti ashirin xaune a waje kafin ya shiga ciki, shara ya sameta take a parlor, ya xauna kan kujera yace "Wel done" murmushi tayi bata ce komai ba, har ta gama ta shiga kitchen ma ta gyara, ya mike ya shiga bedroom yana fitowa ya kalleta yace "Na hada maki ruwan wanka a bathroom...." Xata yi magana wayarta ya dau ring a jaka, karasawa tayi da sauri ta ciro wayar taga Mumy ce ke kiranta, kallonsa tayi sai kuma ta xauna ta daga ta kai kunnenta, daga daya bangaren Mumy tace "Samantha kin shirya tafiya church kuwa?" Turo baki tayi tace "Mumy baki ko tambaye ni ya ciki na ba..." Mumy tace "Ohk ya cikin" kamar xata yi kuka tace "Yana sauki..." Mumy tace "Ohk toh ki shirya kar fa kiyi latti, and make sure yau ma ki tafi gidansu Stellq kar ki kwana ke kadai" Samantha ta kalli Abuturrab dake ta kallonta a hankali tace "Ohk mum" daga haka uwar ta katse wayar, Ta mike tana kallonsa tace "Xan je gida in shirya" yace "Cinye ki xa ayi a nn idan kika shirya," murmushi tayi tace "A'a xan dauko abu ne" yace "Pad?" Xaro ido tayi tace "A'a fah!" Yace "Toh me?" Ta langwabar da kai tayi shiru, yace "Toh tafi kiyi Wankan ki" a hankali tace "Toh" snn ta nufi bedroom din, ko kafin ta fito har ya kai mata jakar kayanta dakin, tana fitowa ta shirya da sauri da sauri tana tsaye gaban mirror xata daura dankwali aka bude kofar dakin, juyawa tayi da sauri, tayi still a gun ganin Ilham, ita kanta ilham kasa motsi tayi bakin kofar, can ta juya da sauri ta fita daga dakin, Abuturrab dake baya gun Gym dinsa ya zagayo don daukan Coke ya ga takalman Sister tasa a bakin kofa, kasa shiga yyi sai gata ta fito, bata ko kallesa ba xata wuce sa ya rikota da sauri yace "me kike nema nn Ilham" fixge hannunta tayi tace "Yaya wacece ita?" Jawota yyi jikinsa yace "listen she's just a frnd lil sis....." Kamar xata yi kuka tace "Noo yaya me yasa kake haka...." Dago kanta yayi yace "Wllh frnd dita ce ilham, trust me.... You've got a decent brother" tace "Amma ae bai kamata ta shigo maka gida har bedroom ba sae kace ba musulma ba" yace "No but she's a Christian, an innocent Christian" shiru Ilham tayi Tana kallonsa, yace "Trust me sis" tabe baki tayi bata ce komai ba, yace "Promise you won't say anything... Even to Khaleesat and Ramlah" turo baki tayi tace "Naji" yayi murmushi ya ja hancinta yace "That's my sis, taho inyi maki introducing dinta, she's a nyc gal" girgixa kai tayi a takaice tace "Noo I hate Christians" daga haka ta wuce ta bar sa gun a tsaye ya bi ta da kallo, can ya shiga parlon yaga Samantha na hada kayanta tana ganinsa kamar xata yi kuka tace "Am sorry doctor...." Yace "For what?" Hawaye ya cika idonta tace "Ur sis...." Murmushi yayi yace "Ae bbu ruwanta ita...." Bata kuma cewa komai ba ta dau jakarta tace "Xan tafi" ya mata wani kallo yace "Sai kin yi breakfast" tace "Noo nayi late for church" yace "toh baxa ki fita ba sai kin yi breakfast ki sha Magani" shiru tayi tana kallonsa, yace "Yes!" Daga haka ya wuce bedroom, xaunawa tayi parlor tayi tagumi, bata ji shigowar Ilham ba sai ganinta tayi parlon rike da tray din abinci, ko kallonta ilham bata yi ba ta ajiye xata fita sai kuma ta nufi bedroom dinsa, Samantha ta bi ta da kallo duk jikinta yyi sanyi, Abuturrab na ganin Ilham yace "Sis kin rufe kofar...." Ta hade rai tace "Breakfast na kawo maka gashi can a parlor" mikewa yayi ya kama hannunta suka fito parlor yana kallon Samantha yace "Meet my Lil sis Rabi'ah but we do call her ilham!" Samantha ta kalleta tana kirkiran murmushi tace "it's nyc meeting you ilham" Bbu yabo bbu fallasa Ilham tace "Same" ta kwace hannunta tayi hanyar kofa, ko kadan Abuturrab bai ji ddin yanda ta amsa ba, ya bi bayanta suka fita a tare, sai da suka yi nisa ya fixgota yace "Why did you answer her that way?" Bluntly tace "Because I don't like her" hade rai yayi yace "Then you don't like me also" da mamaki tace "Toh meye hadin ka da ita ma yaya, ni I hate her...." Wani tsawa yayi mata tayi tsit, strictly yace "Idan kika sake cewa you hate her I won't take it likely with you, me tayi maki?" *Haske writers association*📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 9..... Juyawa tayi, tayi wucewarta ta bar sa gun a tsaye, ya bi ta da wani mugun kallo, can yyi kwafa ya juya ya koma parlor, wayam yaga parlon ya kalli gun da takalmanta suke ya ga ba su wato ta wuce, da sauri ya fita ya bi bayanta, can ya hango ta xata main road sai tafiya take da sauri da sauri, bata san yana bin ta ba har sai da ya isa dab da ita ya fixgo hannunta, ta juyo a tsorace tana kallonsa, kamar xata yi kuka tace "Doctor church xan wuce am almost late" ya mata wani kallo yace "Toh baxa ki ba, uwar me ake k'ara ki da shi a church din?" Shiru tayi tana masa kallo irin ta mamaki, ya ja hannunta ta dinga bin sa har suka iso gida ya kulle kofarsa, breakfast ya nuna mata ya wuce daki, a hankali ta xauna kasa hawaye cike idonta sai kuma ta fara kuka a hankali, sai kusan Karfe goma ya fito shirye cikin kananun kaya as usual, bai ko kalleta ba ya nufi gun breakfast din dake ajiye har lkcn ya xauna ya shiga hada tea, ya debi potatoe da egg kawai ya fara ci, kin dago kanta tayi don har lkcn hawaye take, ya gama cin abinda xai ci ya mike yyi kwanciyarsa kan dogon kujera, ko kukan jini xaki yi baxa ki Church din nn yau ba, ya fadi hakan a xuciyarsa tare da jan tsaki a fili, Har sha biyu da rabi tana wajen a xaune shi ko yyi bacci abun sa hankali kwance, kiran sllh ya sa shi tashi ya mike xaune yana kallon agogo, ga mamakinsa har lkcn tana nan a yanda yake, ya mike bai ko kalleta ba ya shiga toilet ya dauro alwala ya fito ya jima bedroom kafin ya fito don tafiya masallaci, bin sa da kallo tayi har ya fita sai kuma ta fashe da kuka. yana fita ya kulle kofar ta waje yayi tafiyarsa, ana idar da sllh main house ya shiga ya tadda Mumy a bedroom da sistern ta Mariya, ya xauna murmushi dauke fuskarsa yace "Mumy yaushe kika xo?" Tace "Tun daxu, nayi xaton baka ma gidan ne, baka je aiki yau ba knn?" Ya shafa kansa yace "Sae da yamma nake tafiya da week end" tace "Toh Allah ya taimaka, kwana biyu ka guje ni Aliyu" yar dariya yayi yace "Mumy aiki ne ya sha min kai wllh...." Hajiya Mariya tace "Toh Allah rufa asiri...." Mikewa yayi yace "Amma sai da dare xaki wuce koh?" Tace "Anything for me?" Dariya yayi yace "in dai da nyt xaki tafi nasan na dawo daga aiki then sai in maida ki gida" tace "Toh shknn xan jira har ka dawo" daga haka yayi masu sallama ya fita, dakin sisters dinsa ya leka ya gansu suna kallo a system, tsaye yyi bakin kofa ya rungume hannayensa yace "Ba islamiyya yau?" Ramlah tace "Sae anjima" kallon ilham da taki kallonsa yake, ganin yanda ta hade rai tana kallon ya karasa dakin ya dagota, kwace kanta take son yi tana tura hannunsa ya dauketa cak suka fita daga dakin, Khaleesat ta kalli Ramlah suka tabe baki a tare, a downstairs ya direta xata gudu ya fixgota yace "Haba my Lil sis baki son abinda nake so kenan?" Kallon mamaki take masa sai kuma tace "Son ta kake yaya?" Da sauri ya girgixa kai yace "Noo ba haka nake nufi ba, I thought you will also buy the idea of being her frnd too, bata da matsala ko kadan, assignment take kawo min in mata, her home is just few houses away from ours, she's nyc....." Tabe baki ilham tayi tace "Ni dai bana son tana xuwa har cikin parlor da bedroom din ka, baka san shaidan is real ba koh?" Kamar xata yi kuka ta kare maganar, ya danne dariyarsa yace "Na sani mana lil sis.... Amma kinsan ur brother is decent, he can't do anything silly...." Tabe baki tayi tace "Ni dai ina gaya maka" ya ja hancinta yace "Ohk naji my sis, but ki daina daure mata fuska plss kin ji" tace "Na ji" daga haka ya saketa yace "Good of u, kar kuma kice ma su Ramla komai, more especially that stupid Leesat" bai jira cewarta ba ya nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita. Yana isa part dinsa ya ganta xaune har time din tana hawaye, da kamar baxae ce komai ba ya nufi bedroom sae kuma ya dawo yana kallonta ya rungume hannu yace "When ake tashi a church din" kallonsa tayi bata ce komai ba tana share hawayen ta, yace "Answer me!" A hankali tace "Karfe daya" kallon agogo yayi yaga dayan ya wuce, ya koma kofa ya bude yana kallonta yace "Ohk tashi ki tafi, a gaida mutan church!!" Mikewa tayi ta dau jakarta da books ta nufi kofar ta fita snn ta juya tana kallonsa, rufe kofarsa yayi, ta juya a sanyaye ta tafi xuwa gate ta bude a hankali ta fita, gida ta nufa don ta san an tashi a church din, tana isa ta shiga kitchen don yunwa ba kadan ba take ji, doya ta fere ta soya da kwai ta hada tea rabin cup ta dawo parlor ta ci, tana gama ci ta kwanta sai bacci. Hadari ne ya tada ta, ta mike xaune da sauri tana kallon agogo ganin yanda garin yyi duhu, taga karfe biyar har lkcn tafiyarta catechism ya wuce tana bacci, mikewa tsaye tayi jin iska ta hau sama ta rufe windows gaba daya, garin yyi bakikirin, tsoro ne ya kamata tunawa da tayi ita kadai ce fa yau, parlor ta dawo ta rakube jikin kujera lkci daya ruwa me karfi ya sakko, har shidda ruwa ake kamar da bakin kwarya, tsawan da ake ne ya kara rikitata don ko kadan bata son tsawa, wayarta ta dauka ta fara kiran Mumy ta kira ya kai sau biyar no answer, ta kira Abba shi ma haka, ta fashe da kuka ta kife kanta da kujera, har karfe bakwae tana nan a haka, can tayi karfin halin mikewa xata kunna wutan parlor aka yi wani tsawa ta koma da sauri ta rufe fuskarta, ganin parlon yyi bakikirin sbda duhu yasa ta mike cike da karfin hali ta karasa ta kunna sai taga bbu wutan ma, dawowa tayi ta kunna wayarta ta shiga tunanin ko ta hada kayanta ta wuce gidansu Stella kawae, bata tsaya wani tunanin ba ta wuce sama da sauri ta dauko uniform dinta da duk abinda tasan xata bukata ta xuba su jaka, ta canxa kayan jikinta snn ta dawo parlor ta shiga store don dauko umbrella, tana dauka ta fita nan taga ruwan ba na wasa bane ake yi ga iska, kin komawa parlor tayi, tayi ta tsayuwa a balcony, har takwas na dare, hawaye ne ya shiga sakko mata, can ta rufe kofar kawae ta shiga ruwan a haka da umbrella din, mai gadi ya leko daga windon dakinsa yace "Madam ina xuwa cikin ruwan nan?" Ta kallesa tace "Gidan Anty xan je...." Bata jira me xai ce ba ta fice da sauri, haka ta dinga tafiya duk a tsorace tabi ta kankame leman ganin iska na neman dauketa da shi ga walkiya dake ta haskata, ta d'an yi nisa ta ji haushin karnuka, bata kuma san ta ina ne ba, bata san lkcn da ta wurgar da lema da jakar hannunta ba, ta fasa wani ihu ta fara gudu, tun daga nesa ta hango mota na tahowa hakan bai sa ta fasa gudun da take ba, ganin an dallareta da fitila yasa ta tsaya tana rusa kuka, duk tayi jagab, ana bude motar ta ci gaba da gudunta, bin bayanta yyi da sauri har ya isketa ya fixgota, ta fasa ihu ko ina na jikinta na rawa, daga sama har kasa yake kallonta, ta rufe bakinta da hannunta, lkci daya shi ma yayi jagab, yace "Where are you coming from?" Hanyar gidansu kawai ta iya nuna masa, ya ja ta suka nufi gate ya ciro makulli ya bude yana rike da hannunta suka shiga ya bude kofar parlor ya shigar da ita snn ya bude gate ya fita ya shigo da motarsa yana gama parking ya fito ya rufe gate din ya koma parlor tana nn tsaye inda ya bar ta sai rawan sanyi take, kunna wutan parlon yyi ta sunkuyar da kanta, yace "Baki tafi church din kin tsaya can ba da kika ga hadarin kenan?" Shiru tayi bata dago kanta ba, ya tabe baki ya rufe kofarsa ya wuce bedroom ya dauko towel ya dawo ya mika mata, karba tayi ganin taki motsi yace "Go to the bathroom, take off those clothes nd stop shivering" bata ce komai ba ta nufi bedroom din nasa ta shiga bayi ta cire kayan ta daura towel din, jikin gado ta rakube don wani mugun sanyi take ji. Fita Abuturrab yayi bayan ya dauko umbrella ya nufi main house, Mami dake bedroom dinta tare da su Ramlah tace "Har ka kai ta?" Yace "Eh Mami..." Mami tace "Toh meye na yawo da jikakkun kaya kuma..." Yace "Yanxu xan tafi in cire" bai jira tace komai ba ya fita ya shiga dakinsu Ramlah, closet dinsu ya bude yana yi yana waige waige ya dauki wani riga me kauri da yayi kama da na bacci ya rufe press din dai dai lkcn da aka bude kofa, da sauri ya boye rigar a bayansa, Khaleesat ta shigo, daga sama har kasa take kallonsa tace "What are you hiding ya Abuu?" Ya hade rai yace "Nothing" *Haske writers association*📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 10.... Karasowa tayi xata xaga ta bayansa ya maza ya juya ya turata kan gado ta fadi, kafin ta juyo har ya fice ta mike da sauri ta bi sa, a stairs ya kusa cin karo da Ramlah ta je hado ma Mami tea, ya boye rigar a bayansa da sauri, tace "What are you hiding...." Bai tanka ta ba ya sauka ta bi sa da kallo sai ga Khaleesat da gudu tace "Sis meye hannunsa?" Ramlah ta buda hannu alamar bata sani ba, Abuturrab na fita ya dau umbrella dinsa ya nufi part dinsa, yana shiga yasa key kofa don yasan cunning sisters din nasa na iya biyo sa, har lkcn tana durkushe kusa da gado ta takure waje daya, kashe Acn dakin yyi gaba daya ya karaso ya durkusa gabanta ya mika mata rigar yace "Wear this" ba tare da ta kallesa ba ta sa hannu ta karba, ya mike ya bude closet dinsa ya fiddo jallabiya ya fita, tashi tsaye tsyi ta sa rigar taga iyakarsa da kadan ya wuce kneel, bathroom ta karasa har lkcn rawan sanyi take, ta shanya masa towel din ta fito ta koma inda take ta xauna, bayan kusan minti talatin har bacci ya fara daukarta taji muryarsa a kanta, bude ido tayi da sauri ta gansa durkushe gabanta yana sanye da jallabiya hannunsa rike da cup din tea yace "Take!" Sunkuyar da kanta tayi tasa hannu ta karba ya mike ya fita, ba laifi ta sha tea din da yawa ta ajiye wanda ta rage, ta kalli agogo taga goma ya kusa, wayarta ta tuna yana cikin jakar da ta yar a titi, jinginar da kanta tayi jikin gado a sanyaye, sae gashi ya dawo ya rungume hannayensa yana kallonta yace "Toh tashi ki kwanta sarkin yan xuwa church!" Bata ce komai ba ta mike a hankali tana kallon gadon, hawa tayi ta takure gu daya ta kwanta, yayi murmushi ya rufa mata duvet yace "Sae da safe" murya can kasa tace "Thank you" kashe mata fitila yayi bayan ya dau wani bargon ya fita ya rufo kofar, parlor ya koma ya kwanta kan 3seater. Can cikin dare tarin ta ya tada sa, ya dde xaune ganin har lkcn yi take yasa shi mikewa ya nufi bedroom din, bude kofar yyi ya kunna fitila ya karasa ya cire bargon yana kallonta, kakkarwa ya ga tana yi ga numfashinta na sama, ta bude ido tana kallonsa, hannu ya daura kan goshinta yaji xafi sosai, ta rike hannunsa a hankali yace "Are you Asthmatic?" Girgixa masa kai tayi yace "But you have pneumonia?" Bai jira tace komai ba ya mike ya bude closet ya fiddo babban sweater dinsa ya dawo ya dagota ya sa mata da kan shi ya kwantar da ita, kallonta ya tsaya yi yana tunanin taimakon da xai mata ganin yanda numfashinta ke yi, mikewa yyi ya dauko rub ya dawo ya bude zip din sweatern ya mika mata yace "Tashi ki shafa a chest din ki, it will help...." Jin bata ce komai ba ya bude ya diba sai kuma ya rasa yanda zai yi, imagine yyi da daya daga sisters dinsa ne ke shoe din nn ya xae yi, daga rigar xae yi ya shafa masu, yana wannan tunanin kawae ya daga rigar baccin jikinta ya sa hannu ya fara shafa mata rub din all over her body, hannunsa ta rike da sauri tace "Doctor..." A hankali yace "Yes am only being the doctor I am" bai kuma sauraranta ba ya shafe duk jikinta da man xafin, rufe ido tayi taki budewa, yana gama ya xuge xip din sweatern ya lulluba mata bargo murya can kasa yace "Go to sleep" bata ce komai ba bata kuma bude idon ba ya mike ya kashe fitilar ya fita, har bakwai bata tashi a bacci ba shi ma bai tasheta ba sanin jiya bata wani yi bacci ba, wanka yyi ya fito ya gama shirinsa a dakin sannan ya dawo parlor ya kunna laptop yana dube dubensa, can ya mike ya shiga kitchen don hada coffee, yana fitowa ya ga kofa a bude ya kalli kofar bedroom ya ga a bude shi ma, da sauri ya karasa bedroom din don a tunaninsa tashi tayi, tayi wucewarta, still yayi bakin kofa ganin khaleesat tsaye, ta juyo tana masa wani irin kallo, duk ya daburce, juyawa tayi xata wuce ya rikota ya ja ta suka fita balcony yace "look leesat, she's just a frnd.... Bata da lafiya ne wllh..." Kamar xata yi kuka tace "Ni dai ba ruwana, ko nace maka wani abu ne.... Ni dai bance komai ba, ba ruwana" marairaice mata yyi yace "Baki yadda da brothern ki ba knn?" Wani kallo ta jefa masa ta warce hannunta tace "Eh ni ban yrda da kai ba kuma, dama shi yasa this days baka son muna xuwa wajen ka koh?" Hade rai yayi yace "I said she's my patient, are you daft?" Tabe baki tayi ta juya tayi wucewarta, da sauri ya bi ta ya fixgota fuskarsa daure yace "One word about what you just saw will mean you spelling dooomm" saketa yayi ya koma parlonsa, bai dade da shigowa ba peter ya kawo masa breakfast, takwas saura 'yan mintuna ya shiga bedroom bayan ya gama cin abinda xae ci na abincin da aka kawo masa, xaune ya ganta kan gado ta lulluba da bargo, tana ganinsa ta sunkuyar da kai, ya karaso bakin gadon yana kallon gashinta da yyi scatter all over, yace "Good morning" kallonsa tayi tayi murmushi bata ce komai ba, cire bargon jikinta yyi ta jawo da sauri ta rufe, buda ido yayi sai kuma ya d'an yi murmushi yace "ohk.... How's ur health?" Kai ta gyada masa ya juya ya fita, mikewa tayi bayan ta cire bargon ta nufi bathroom, ta tara ruwan xafi ta tsirka sannan ta wanke fuskarta, ta dau Listerine mouth wash/freshner dake bayin ta wanke bakinta snn ta fito, tsaye ta gansa dakin gaban mirror ta juya masa baya da sauri, karasawa yyi bayanta ya dafa shoulders dinta ya juyo da ita, ji tayi kamar ta nutse cikin sarkewar murya tace "Ina kwana...." Kallon kwayar idonta yake sai kuma yayi murmushi bai dai ce komai ba, ta sunkuyar da kanta, saketa yyi yace "xan tafi aiki yanxu....." Da sauri ta dago tana kallonsa tace "Nima xan je sch" kallon agogo yayi da sauri ita ma ta kalla, kamar xata yi kuka tace "Why did you not wake me" ya langwabar da kai yace "Coz you are sick" tace "Ni na samu lafiya.... I can still go" yace "Toh uniform din ki fa?" Xaro ido tayi tunawa da tayi ae fa ta jefar a titi, a hankali tace "Na yadda jakar a hanya doctor" shiru yyi yana kallonta snn yace "Ohk, let me get it for you" daga haka ya juya ya fita, ta koma a hankali ta xauna kamar warce ta tuno abu kuma ta mike ta shiga bathroom ta fara hada ruwan wanka, bayan kusan minti sha biyar ta fito daure da towel dinsa, xaro ido tayi ganinsa ta juya da sauri xata koma bayin ya dakatar da ita ta hanyar cewa "do I look like a monster!" kasa shiga bayin tayi ta kuma kasa juyowa, ya tsura mata ido daga sama har kasa, haka kawae yaji ya kasa tsayuwa, can ta juyo a hankali jin bai kuma cewa komai ba tana kallonsa, dauke kai yayi gabansa ya shiga faduwa, ta karaso a sanyaye tace "Am...am sorry!" Yayi karfin halin kallonta yace "Better, uniform din ki sun jike, kawai ki bari gobe ki tafi schl din" shiru tayi bata ce komai ba, ya dauke idonsa yace "Let me get you something to put on, but before then...." Gaban madubi ya nufa ya nuna mata lotions hadda na gashi yace "You manage this" sunkuyar da kanta tayi ya juya ya fita. Main House ya tafi ya ga Mami ce kadai a parlor tana kallon wani program, kanninsa duk sun tafi boko, ta kalli agogo tace "Baka tafi aikin ba har yanxu Haiydar" yace "Ehh yanxu xan tafi, wasu takaddu da na ba ilham xan karba" daga haka ya wuce sama ta bi sa da kallo, yana shiga ya kulle dakin ya bude closet dinsu, ganin tafi son saka dogayen riguna ya fiddo mata da wani bakin abaya da ya gani gogagge da veil dinsa, har da sabbin inner dinsu ya dauko mata, tunanin yanda xae fita da kayan ya fara yi, can ya leka window sai kuma ya dawo ya dau towel dinsu dake baje a kan gado yayi wrapping din kayan ya koma gun windown ya jefar ya rufe wajen, snn ya dawo ya bude bedside drawer ya fiddo full scap sheet dinsu har uku ya linke yana rike da shi a hannu ya fita, ya sallami Mami da ta bi sa da kallo ya fita, yana xagawa ya dau kayan ya nufi part dinsa, xaune ya sameta gaban madubi har lkcn tana shafa mai, kallo daya yayi mata ya dauke kai ya ajiye mata kayan kan gado ya juya ya fita, cikin few minutes ta ga gama shiryawa ta fito ta samesa xaune a parlor, sosai kayan suka mata kyau kamar balarabiya haka ya dinga kallonta har ta karaso kanta a kasa tace "Thank you Dr!" Yace "Welcome, ga breakfast" girgixa masa kai tayi tace "A'a, gida xan tafi" d'aga kafada yyi yace "As you wish, uniform din suna balcony" tace "Toh" snn ta nufi kofa ya bi ta da ido, sae da ta bude kofar snn ta juya ta kallesa suka hada ido, dauke kai tayi da sauri ta fita, ya lumshe ido na kusan minti bakwai sai kuma ya mike ya dau makullin motarsa ya fita. Ko da ta isa gida bata damu da ta kunna wayarta ba sanin ba lallai ya kawo ba, duk da tasan kila su Mumy na ta kiranta, gabanta ya fadi tunawa da tayi Mumy xata iya kiran gidan su Stella su ce bata je ba, mikewa tayi da sauri ta fita xuwa gun mai gadi tace "Plss ka aran min wayar ka idan kana da flashing power xan kira su Mumy ne" mika mata yayi ta karba, tana flashing ba a jima ba kiran Mumy ya shigo ta daga tace "Mumy!" Daga daya bangaren Mumy tace "Samantha me ya samu phone din ki" kamar xata yi kuka tace "Ya fada ruwa" Mumy tace "How manage, me ya sa baki tafi schl ba" tace "Mumy am coughing, am not feeling fine" Mumy tace "Baki je gidansu Stella din ba kenan?" Tace "Ehh mumy am at home" Mumy tace "You are covered with the blood of Jesus my daughter, don't worry gobe ina hanya, ki dau kudi ki siyo maganin tari" a hankali tace "ohk Mumy" daga haka suka yi sallama, Samantha tayi kwanciyarta, sai can kusan sha daya ta tashi ta fara gyara ko ina na gidan kafin sha biyu ta gama, ta wanke uniform dinta ta shanya snn ta shiga kitchen nan ma ta gyara ko ina, tunanin abinda xata girka ta shiga yi, can tayi deciding tayi jollof rice da sauce din cow meat sai fried plantain anjima, kafin ta fita ta hada tea ta soya kwai ta fito ta ci ta kwanta sai bacci, ba ita ta tashi ba sai hudu, ta kunna TV tayi kallon kusan awa daya, mikewa tayi jin tana jin yunwa ta shiga kitchen don yin girkin, da yake akwai komai a gida kafin karfe shidda da rabi ta gama tayi slicing lettuces, tomatoes, cucumbers, onions, and carrot ta ajiye su gefe, ta debi abincin da xata ci ta fita xuwa parlor, ajiyewa tayi ya huce ta tafi wanka, tana daure da towel ta dawo ta dau abincin ta, tana fara ci Abuturrab ya fado mata haka kawai taji tana son kai masa duk da ba da yawa tayi ba, kallon agogo tayi taga bakwai ya gota, tasan ya dawo aiki yanxu, bata wani ci abincin da yawa ba ta mike ta koma kitchen ta xuba masa shinkafar a warmer, ta debi sauce din a wani cooler, ta dau wani transparent breakable bowl ta xuba masa vegetables din ta rufe, ta sa su gaba daya a basket snn ta dawo parlor ta ajiye, sama ta tafi xuwa saka kaya, ta shirya cikin doguwar riga me tsantsi, ta daura veil a kai ta fita. *Haske writers asso* 📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 11.... Tsarguwa tayi da irin kallon da mai gadinsu ke mata, ta hade rai tana rike da basket din abincin tayi ficewarta, cikin minti sha biyar ta isa gate din gidan, sai kuma ta tsaya tana tunanin kila ma bai dawo ba, karasawa gate din tayi ta tura a hankali taji a bude, ta leka compound din ta ga motarsa a space din mota biyu dake wajen, shiga tayi kamar mara gaskiya ta rufe gate din snn ta wuce parlor, a bude ta tadda kofar ta shiga da takalmanta tana kalle kalle, ta ajiye basket din hannunta ta xauna jin kamshin sabulu da ya gauraye ko Ina yasa tayi tunanin kila wanka yake, ta kusa minti bakwai xaune ta ji kamar foot step, mikewa tayi tana kallon kofa, sae kuma ta juya da sauri ta nufi bedroom dinsa ta bude kofar ta shiga ta rufe, kasa barin bakin kofar tayi kuma ta kasa juyowa, taji an bude kofar bathroom duk da haka bata juyo ba, ji tayi an juyo da ita ta daga kai tana kallonsa, daure yake da towel a waist dinsa, ta sunkuyar da kai, yayi murmushi yace "No church yau?" Kasa magana tayi, can cikin in ina tace "Dama...dama yanxu xan tafi, I brought you food... Yana parlor" kallonta kawai yake ko kiftawa bai yi, duk ta rikice ta juya da sauri, ya kuma juyo da ita taki dago kanta, murya can kasa yace "You brought me food..." Tana gyada kai kamar munafuka tace "Yess, yes I taught you will like it..." Dago kanta yayi a hankali yace "Thank soo much..." kasa kallonsa tayi, shi ko sai kallon bakinta yake, ta juya a hankali tace "Sae da safe" bata jira cewarsa ba xata bude kofa sai jinta tayi a jikinsa, ta xaro ido tace "Doc...." Bata kai karshe ba ta ji bakinsa cikin nata, a tsorace take kallon kwayar idonsa, ya lumshe ido ya jinginar da ita jikin kofa ya shiga kissing dinta a hankali, rikicewa tayi ko ina na jikinta ya dau rawa ta kuma kasa kwace bakinta, a hankali ta fara silalewa kasa ya rungumeta a bare chest dinsa har lkcn yaki cire bakinsa a nata, sun kusa minti shidda a haka aka bude kofa can parlor, wani karfi ya xo mata ta turasa xata bude kofar dakin ya jawota jikinsa ya kankameta, saukan hawayenta ya ji kirjinsa, ya sa ma kofar key jin muryar Mujaheed, xamewa tayi kasa ta hade kai da gwiwa, bubbuga kofar dakin Mujaheed yayi yana cewa "Are you there Aliyu?" Abuturrab bai tanka sa ba ya bude press ya fiddo jallabiyarsa ya sa ya cire towel din jikinsa ya kai bayi ya fito yana kallonta don har lkcn bata dago kanta ba, bude kofar yyi ya fita ya rufe, Mujaheed da har ya koma parlor yace "Meye na rufe kofa a bedroom kamar mara gaskiya?" Abuturrab na shafa kansa yace "Su Ramla ke damuna" Mujaheed yace "Ohk, Mum ce ta aiko Amira gun Mami.... Shine nayi dropping dinta, and we are leaving yanxu" Abuturrab yace "Ohk xan shigo anjima idan na fito" Mujaheed yace "kamar gaske" daga haka ya nufi gun abincin dake ajiye parlor ya bude yace "Whose food is this" Abuturrab yace "Mine" spoon Mujaheed ya dauka ya debi abincin ya kai baki yana cewa "But tuwo Mami ta xuba mana wai sai mun ci Ashe akwai wnn..." Abuturrab bai tanka sa ba, mujaheed ya xaro ido yace "Kai amma Mami da kanta tayi girkin nan koh..." kara kai wa baki yayi yana lumshe ido yace "Ae sai na koma an xuba min nawa, wnn dadi haka" daga haka ya nufi kofa Abuturrab ya dakatar da shi da sauri yace "look siya nayi ba a gida aka yi ba, kasan ni bna cin tuwo" Mujaheed ya dawo yace "Toh bari in dauko plate..." Kitchen ya tafi ya dauko plate ya dawo ya debi abincin da sauce da vegetables ya xauna ya fara ci yana ta santi, Abuturrab ya xauna ya kunna tv amma duk hankalinsa baya kai, da ya tuna incident din moment din sai gabansa ya fadi, Allah Allah yake Mujaheed ya wuce, ae ko sai bayan kusan minti sha biyar Mujaheed ya bar gidan, Abuturrab ya rakasa ya dawo, kasa shiga bedroom yayi duk jikinsa yayi sanyi, can yayi karfin halin bude kofar a hankali, ganinta yayi durkushe yanda ya fita ya bar ta har lkcn bata dago kanta ba, ya karasa kusa da ita a sanyaye ya durkusa amma ya kasa dagota, lumshe ido yayi ya dafata yace "Am..am sorry I didn't mean...." Mikewa tayi da sauri idonta ya kumbura don kuka ta juya xata fita ya tashi ya rikota kan yace komai ta fashe da kuka sosai har da shessheka, rikicewa yayi yace "Plss kiyi hakuri it's not intentional, I..." Fixge hannunta tayi ta fice da sauri, ya bi bayanta, tana ganin haka ta saka gudu ya bi ta har suka fita gate, hanyar gida ta dauka tana gudu iya karfinta shi ma kuma bai fasa bin ta ba, tana isa dai dai Inda ta saba jin haushin kare ta tsaya cak tana maida numfashi ganin karnuka har biyu, suna ganinta suka fara nufota suna haushi, juyawa tayi a rikice ta fara gudu ta nufi gunsa don tuni ya tsaya ganin karnukan tana isa gabansa ya rungumeta tayi tsit sai dai duk jikinta rawa yake, a hankali ta xame jikinta da kyar tace "Ka raka ni plss" hannunta ya kama ya nufi gate ta ce "No plss gida xan wuce" yace "Not when you are still angry at me" da sauri tace "No am not angry, ni ban yi fushi ba..." Xai yi magana fitilar mota ta dallarosu daga nisa, da sauri ta boye fuskarta a jikinsa don mutane daddaya ne basu san Mumynta anguwar ba, suna a haka har motar ya wuce ta dago da sauri tace "Doctor ka rakani plss" a hankali yace "Ke daya xa ki kwana?" bata bari sun hada ido ba tace "A'a Antyna tana nan" kama hannunta yyi ya fara tafiya xuwa gidan nasu, har suka isa bbu Wanda yace komai, shi dai duk jikinsa a sanyaye yake, bata ko kallesa ba xata shiga gate yace "Frnd..." Shigewa tayi abun ta ba tare da ta juyo ba ta rufe gate din, juyawa yayi ya bar gun ya koma gida. Yana isa gida ya xauna parlor yana kallon abincin da ta kawo masa, can ya mike ya bude abincin ya kusa minti biyar rike da cover din warmer din yana kallon abincin, can ya dau spoon din da Mujaheed ya ci ya debi abincin ya kai baki, a hankali ya dinga taunawa, sai a snn ya gane ma'anar santin da Mujaheed ya dinga yi, wato the food was just perfect, so sweet, sosai yayi mamakin iya girkinta, plate ya dauka ya xuba abincin da vegetables sae sauce din naman, mancewa yayi da abinda ya faru bai ajiye plate din ba sai da ya cinye abincin, murmushi yayi underneath his breathe yace "Waow, she's a nyc cook" bude kofarsa aka yi ya daga kai da sauri Ilham ta shigo ta karaso kusa da shi tace "Ya Turab towel din mu muke ta nema bamu gani ba....". Kallonta ya tsaya yi kamar bai gane me take cewa ba, tace " Ya Abuu" ya ajiye plate din hannunsa yace "Toh ni ta ina xan san inda towel din ku yake...." Tace "Wa ya kawo ma abinci?" Yace "I bought it" mikewa yayi ya shiga daki ya bar ta wajen a tsaye, tabe baki tayi ta juya ta fita. Kasa sukuni Abuturrab yayi, duk ya tuna abinda ya faru sai ya ji haushin kansa, mikewa yayi daga kwancen da yake misalin tara saura ya fita, ya d'an yi xuke xukensa ya dau motarsa ya fita, gidansu Saudat ya nufa, har ya mance rabonsa da ita, yana parking kofar gidansu ya sa mai gadi yayi masa sallama da ita, bayan kusan minti goma ta fito, ya dinga kallonta har ta karaso babu yabo bbu fallasa ta rungume hannayenta tana kallonsa, yayi murmushi yace "Kin mance ni kwana biyu" wani kallo tayi masa tace "Dole kace haka, tunda kun bata da sabuwar budurwar ka shine ka yo guna yau" yace "Haka kika ce" tace "Eh mana..." Ya tabe baki yace "Toh shknn, will you escort me" wani kallo ta kuma jefa masa tace "Ga mara mafadi ko, dama abinda ya kawo ka knn na sani, in rakaka dabar ku, to baxan je ba" yace "Seems kin fara gajiya da ni Saudat, naga alama you want breakup...." Tace "Toh meye maraban dambe da fada, da wannan sharenin da kake for months ae gwara ma breakup din....". Yace "Alryt..... Good you told me that" daga haka ya shige motarsa ya kara gaba, sosai ya ji ransa ya baci ya koma gida yayi kwanciyarsa. Washegari Tuesday throughout bai ga Samantha ba, duk da xaman da ya dinga yi waje bayan ya dawo aiki, laraba ma ta xo ta wuce bai ganta ba, wasa wasa har Friday, ya rasa dalilin da yasa ya damu haka, ko abinci sai ya tilasta kansa yake ci, he just can't say how much he missed her, misalin hudu na yamma ya kasa daurewa ya dau hanyar gidansu, can gaba da gate dinsu ya tsaya jikin flowern gidansu kamar me jiran wani, bude gate din aka yi Mum dinta ta fito suka yi ido hudu, har ta dauke kai ta kuma juyowa ta kallesa, shi ko ya fara danne dannen waya, Komawa ciki matar tayi ta fito tare da mai gadi tace "Habu wannan fa?" Mai gadin ya kallesa ya karasa Inda yake yace "Malam kana neman wani ne" Abuturrab ya kallesa yace "Ehh abokina nake jira a can gidan" ya fadi hakan yana nuna wani gida, matar tace "Toh ae ba wajen jira bane nn, jikin gidan mutane kake, ka kara gaba kadan malam" Kallonta kawae Abuturrab yake, ta hade rai tace "Ko flawan uban ka ne kke kallo na haka" bude gate aka yi duk suka juya, Samantha ta fito rike da jakar uwar tata, tana sanye da Doguwar riga amma na atamfa ta yafa yellow veil kallan atamfar a kanta, Ido hudu suka yi da shi ta kasa motsi Inda take, Cike da masifa uwar tace "Kai ni fa na fi ka hauka bani da kyau, before the count of 5 get out from this premises, it's my husband's not ur father's" Abuturrab yace "Kiyi hakuri Mama ya ma ce min ba nan bane can gaba ne" daga haka ya kalli Samantha cikin ido snn ya juya ya bar wajen, ta bi sa da kallo uwar ta fixgo hannunta tana cewa "Mahaukaci kai" Ilham ta warce hannunta daga rikon da Khaleesat tayi mata tace "Meye ne baxa ki iya gaya min parlor ba sai kin jawo ni nan" Khaleesat tace "It's about ya Abuu, and bana son Sis Ramla ta ji, I know she might tell Mami...." Ilham tace "What about him?" Khaleesat tace "That boys qtr he is staying is doing him more harm then good, kin san me na gani ranan?" Ilham tace "Meye kika ga" khaleesat ta bata fuska tace "I saw a lady in his bedroom...." Ilham tayi shiru sai kuma a hankali tace "I don't know what yaya Abu is turning to now" kamar xata yi kuka ta kare maganan, Khaleesat tace "Ke ma kin taba ganin ta koh?" Ilham ta gyada kai tace "Ehh, but warce kika gani ya take?" Khaleesat tace "Tall, fair, slim, sai kyan dan maciji" Ilham tace "Yess ita ce...." khaleesat ta dafe kanta tace "Toh ya xa muyi yanxu?" Ilham na gyada ksi tace "nasan maganin yar iskan, kuma fa arniya ce ba ma musulma ba" khaleesat ta xaro ido tace "What?" Kamar xata yi kuka tace "Me yasa ya Abu ke haka...." Kwafa ilham tayi tace "I know what to do" daga haka ta fita Khaleesat ta bi ta tana cewa "Toh me xa mu yi" washegari Saturday bayan azahar Abuturrab ya tafi gun aiki, su kuma su Ilham da khaleesat na ta kai komo part dinsa tun safe don ko islamiyya basu je ba duk suna jiran ganin xuwan Samantha amma har dare shiru, Ranan lahadi yana cikin bedroom su kuma suna xaune daga balcony dinsa, Khaleesat na neat din table cloth duk don kada ya xargi komai idan ya fito ya gansu, shi kam ko sanin suna gun bai yi ba, Ilham ce ta fara jin motsin gate ta mike da sauri haka ma khaleesat, a hankali ta turo gate din ta shigo sae dai bata bar kusa da gate din ba, suka labe jikin pillar suna kallonta, Abaya ce jikinta ta daura bakin dankwalin a kanta, hannunta rike da bible, jira suka dinga yi ta karaso amma bata karaso ba, sae jujjuya bible din hannunta take kamar Mara gaskiya tana kalle kalle, gani suka yi ta juya a hankali xata fita, ilham tace "Keeeee" cak ta tsaya sai kuma ta juyo da sauri tana kallonsu, duk suka fito suna mata wani matsiyacin kallo, ilham tace "In tambaye ki mana, nan kin ga yayi Kama da club?" Shiru Samantha tayi tana kallonta, khaleesat ta mata tsawa tace "Ke kurma ce xaki dinga kallonmu haka, idan baki fadi me ke kawo ki gidan nan ba sai mun yi maki shegen duka" Sauke idonta tayi bata ce masu komai ba, Ilham ta fincikota tace "Are you daft, ki fadi me ke kawo ki gidan nan kar mu maki shegen duka" hawaye ne ya cika idonta cikin rawar murya tace "Assignment yake taya ni....." Khaleesat kmr xata yi kuka ta dungureta tace "Assignment din uwarki, kina dai xuwa koya ma yayanmu iskanci koh? Ance maki prostitute ne shi kamar ki...." Xaro ido Samantha tayi tace "Ni ba prostitute bace...." Ilham tace "Karya kike, you are a prostitute...." Ta fashe da kuka tace "Am not a prostitute believe me...." Shakota khaleesat tayi a fusace tace "Wllh wllh daga yau kika sake xuwa kusa da gate din gidan nan sae mun cire maki hakora, kina xuwa kina lalata mana yaya, arniya kawai" sosai Samantha take kuka cikin raunin murya tace "Ni ba arniya bace, I have my religion, I am a Christian...." Ilham tace "Toh suwaye Christians din idan ba arnaye ba, ke katuwar arniya ce......" Bude kofa aka yi duk suka juya da sauri, kallon mamaki yake masu gaba daya, Khaleesat ta saketa da sauri, ya karaso a tsawace yace "Meye haka?" Khaleesat da ilham suka xumburo baki, ita kuwa Samantha banda kuka babu abinda take, duk ya rikice ya kuma yi masu wani mugun tsawa yace "Meye haka nace?" Ilham ta murguda baki tace "Warning muke yanka mata ta bar xuwa....." Hannu ya kai xai dalla mata mari ta bar gun a guje khaleesat ta bi bayanta, da sauri ya bi Samantha da har ta bude gate, ya rikota ta fashe da kuka tana son kwace kanta, ya ki saketa yace "No plss kiyi hakuri frnd, listen to me...." Cikin kuka tace "They called me a prostitute....." Lkci daya idonsa ya kada ya ma rasa abinda xae ce mata kawae ya jawota jikinsa yace "You are not dear....." Ganin yanda take kuka ya ja ta xuwa parlor, ya fi minti ashirin yana aikin lallashinta, ya lura tana da rauni sosai, ta maimaita an kirata prostitute ya fi sau biyar, da kyar ya samu tayi shiru yana rungume da ita, a hankali tace "And ni ba arniya bace, I have my religion, I am a Christian" shiru yayi bai ce komai ba, sun fi wani minti goma a haka snn ta xame jikinta a hankali ta mike ta kallesa tana goge fuskarta, mikewa yayi shi ma ya kamo hannunta yace "Plss am sorry on behalf of those stupid gals, I promise to teach dem a lesson" girgixa kai tayi tace "Ni basu min komai ba" daga haka tayi ficewarta a parlorn. Lumshe ido yayi ya bude shi ma ya fita, main house ya nufa fuskarsa daure, Ramlah kadai ce xaune parlor tana assignment fuskarsa daure yace "Ina su Rabi'ah?" Sama ta kalla tace "Suna sama" sama ya nufa ya bude dakinsu bbu su, ya bude na Mami ya gansu xaxxaune gefen ta. By _Khaleesat Haiydar_ hope this is enough😅 *Haske writers asso*📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 12___13 Hade rai yayi ya xauna Mami dake kallonsa tace "Ya aka yi Aliyu?" Kin cewa komai yayi Ilham da khaleesat suka yi lamo jikinta, lkci daya duk ya jefa masu wani arnen kallo ya mike kamar wanda aka tsikara ya fice daga dakin kamar xae tashi sama, Mami ta kallesu tace "Kun nemi tsokanarsa koh?" Ilham ta turo baki tace "Ba abinda muka yi masa" har magrib su ilham basu yarda sun bar dakin Mami ba, nan ta tabbatar ba karamin laifi suka yi ma yayan nasu ba, bbu yanda bata yi da su ba su fadi me suka yi masa suka ki magana, har part dinsa Mami taje bayan Isha ta shiga har bedroom dinsa ganin baya parlor ta gansa xaune gefen gado hannunsa rike da waya, karasawa tayi tana kallon kofar bathroom jin k'aran washing machine, ya ajiye wayar hannunsa yace "Mamina...." Mami tace "dama akwai washing machine a nan?" Yace "Ehh akwai...." Tace "Wanki kake?" Yace "No, just singlets..." Xaunawa tayi tace "Laifin me su ilham suka maka ne wai?" Ya shafa kansa yace "Ya wuce Mami...." Mami ta tabe baki tace "Toh ku kuka sani, naga tun daxu baka shigo ba" yace "Ehh Mami dama yanxu xan shigo" tace "Ohk, toh xan samu a d'an siyo min fruit?" Ya kalleta yace "Toh Mami" mikewa tayi tace "kar ka siyo lemo just apples, grapes and watermelon" yace "Toh Mami, yaushe Abba xai dawo" tace "Baka da numbersa ne?" Murmushi yayi tace "Atoh" daga haka ta nufi kofa ta fita, mikewa yayi ya shiga bathroom ya kashe machine din ya fito da har xai dau makulin mota ya fasa don bbu wani nisa ya dau kudi kawai ya fita, kamar bai son tafiyar yake yi, duk bai da sukuni, yana isa bakin hanya dai dai gun masu saida fruits yayi xaman sa har sai da aka tambayesa mai xai siya, ya kalli mutumin ya gaya masa, wata mota ce tayi parking dai dai gun, ya dinga kallon motar har aka bude, gabansa ya fadi ganinta ta fito, bata ko lura da shi ba ta taho gun mai sayar da fruits din, mikewa yayi yana kallon cikin motar yana son sanin ita da waye, ido hudu yayi da Mum dinta da ta hakikince bayan mota, da ganinta kasan daga church suke, dauke kai yayi ya taka xuwa gun mai fruit din da har ya gama xuba masa nasa a leda yana xuba mata nata, kallonta kawae Abuturrab yake ganin mood dinta kamar mara lafiya yasan kuma tun abun da ya faru daxu ne, lkci daya kamar ance ta juyo ta juyo, kasa daina kallonsa tayi sae shi ne ya dauke ido sanin uwarta baxa ta rasa kallon su ba, ai ko kamar ya sani kallon nasu take kamar idanuwanta xa suyi magana, xagawa yayi ya dau ledan fruits dinsa ya sa hannu aljihu ya ciro kudi hade da wayarsa ya d'an saci kallon uwar ta yaga fa har lkcn kallon direction dinsu take, yi yayi kamar xai mika ma mai fruits kudi, ya tsaya daga bayanta cikin dubara ya kamo hannunta ya saka mata wayarsa a ciki, snn yayi saurin mika ma mai fruits kudinsa ya juya ya bar wajen, ita kanta jikinta ya bata mum dinta na kallon gun duk ta tsorata kada ace taga sanda ya bata waya, tana karban ledan fruits din tayi saurin jefa wayar a ciki ta basa kudinsa sannan ta juyo ta nufi gun mota, tana shiga motar mumy ta jefo mata tambayar da ya tsorata, "Samantha kin san wannan mutumin ne?" Cewar mumy kenan tana kallonta ido a zare, Samantha da Gabanta ya shiga faduwa tace "Wani mutum mumy?" Uwar tace "Wanda ya siya fruits yanxu" Samantha ta girgixa kai da sauri amma bata ce komai ba don bata iya karya ba, cike da masifa uwar tace "Karya kike, I saw the way he was looking at you, ina raba ki da non believers din nan baki ji ko, meye hadin ki da musulmi?" Hawaye cike idonta tace "Kiyi hakuri Mumy...." Wani tsawa tayi mata tace "Sorry for ur self, stupid girl kawai, ina cross din wuyar ki, Kin kara cirewa koh?" Hawaye cike idonta tace "Na mance shi gaban mirror" har suka isa gida masifa Mumy ke mata, Ta kankame ledan fruits din Don tasan kashinta ya bushe idan ta karbi ledan ta ga waya, a dinning ta ajiye ledan tayi saurin ciro wayar ta boye a rigarta ta wuce sama da sauri. Misalin sha daya tana durkushe gaban gadon ta hade hannayenta biyu idonta lumshe tana addu'a xata kwanta taji vibration din wayar a karkashin pillow da ta ajiye, mikewa tayi da sauri ta isa gun kofa ta sa key snn ta dawo ta dau wayar, number ne bbu suna, a hankali ya daga ta kai kunne, daga daya bangaren taji ance "Hellow frnd!" Murya can kasa tace "ina yini" yace "Lafiya lau, baki yi bacci ba?" Ta gyada kai kamar yana ganinta tace "xan yi yanxu" cikin sanyin murya yace "Ohk, am sorry dear for what happened in the afternoon, plss Kiyi hakuri...." Da sauri tace "Ae ya wuce" yace "No nasan it's still touching you, for my sake kiyi hakuri don Allah" hawaye ya cika idonta a hankali tace "I've already forgiven and forget.... My religion prohibit us from not forgiving, cause we are also being forgiven by the almighty God" ya lumshe ido yace "Ohk my dear, thanks much, ya daren?" Tace "It's nyc..." Yace "Good, gobe xa ki sch koh?" Tace "Ehh" yace "Toh sai da safe...." Da sauri tace "Toh ina xan baka phone dinka?" Yace "No, na baki so that xan dinga jin muryar ki" murmushi tayi tace "Muryata kuma?" Yace "Yeah dear, ur sweet voice..." Xaro ido tayi, tayi dariya tace "Ni ba ruwana, byee" murmushi yayi ya lumshe ido jin dariyarta, cikin sanyin murya yace "Ohk dear, sleep tighttt" a hankali tace "Thank you...." Daga haka ta katse wayar, kwanciya tayi tana kallon wayar kirar Infinix, ganin a bude yake ta shiga gallery, hotunan sisters dinsa ta fara cin karo da, gabanta ya fadi sosai tana kallonsu, A hankali ta dinga wuce su, yawanci duk hotunansu ne, sai na mami tana gani kuma ta gane mum dinsa ce sbda kamar da ta gani, wani hotonsa ta gani yana sanye da white Coat dinsu na likita, wuyarsa sakale da stethoscope fuskarsa dauke da murmushinsa mai kyau, sosai hoton yayi kyau, pink lips dinsa ta tsura ma ido, lkci daya incident din ranan ya fado mata gabanta ya fadi sosai, da sauri ta wuce hoton, haka tayi ta kallon hotuna har suka kare, ta lumshe ido daga haka bacci ya dauketa wayar na kwance kirjinta. Washegari da asuba vibration din wayar ne ya tada ta, mikewa xaune tayi da sauri, ta jawo wayar tana kallo taga number jiya ne, a hankali ta d'aga ta kai kunne, daga daya bangaren taji yace "still sleeping" murya can kasa tace "Na tashi" yace "Noo na tashe ki dai" murmushi tayi yace "Alryt, na dawo mosque shine nace bari in tashe ki duk da nasan bbu abinda xa ki yi....." Tace "Xan yi addu'a mana" yace "Wani addu'a?" Tace "Wanne kai kayi yanxu?" Yace "Sallah naje masallaci nayi mana" tace "Toh nima yanxu xan yi nawa addu'an" ya tabe baki yace "Toh ayi addu'a lfya" tace "Ohk thank you..." Katse wayar yayi ya ajiye yana girgixa kai. Mikewa tayi ta durkusa jikin gadonta ta hade hannayenta ta lumshe ido, ta kusa minti goma a haka kafin ta mike ta shiga bathroom ta wanke baki ta hada ruwan wanka tayi ta fito, bata 6ata lkci gun shiryawa cikin uniform dinta ba ta fito ta shiga dakin mumy ta ganta xaune kan study table dinta idonta sanye da glass bible a gabanta, karasawa tayi tace "Ina kwana Mumy" Mumy ta rufe Bible din tace "Lafiya lau, kin yi addu'a?" Ta gyada kai tace "Nayi" Mumy tace "Yaushe ne waec din naku?" Tace "Ba na gaya maki ba, it's on Monday" Mumy tace "Good, kina karatu dai koh" tace "Ina yi Mumy" daga haka ta fita, sai kusan takwas da rabi ta bar gida don revision kawai suke a sch, a motar gidansu xa a kai ta sch din, suna isa layin gidansu Abuturrab sai ga shi shi ma ya fito da mota, bai yi gigin hawa kan titi ba ya jira su fara wucewa, gaba daya ya tsura ido ya ga Inda xai ganta cikin motar, dama ita ma tun daga nisa ta hangosa, a hankali ta sauke glass har suka iso dai dai gate din, ta wara ido hade da d'aga masa hannu, kashe mata ido daya yyi, ta xaro ido hade da toshe baki kar tayi dariya, haka ya bi motar da kallo har suka wucesa, ya lumshe ido ya karasa motarsa ya shiga ya dau hanyar gun aiki, Tun daga ranan basu sake haduwa ba, bai kuma damu ba don ko da yaushe cikin waya suke, ita kuwa kwata kwata ta daina bin hanyar gidansu don ma kada su hadu, ta gwammace taje ta xagaya duk da nisan tafiyar don ita tsoron sisters dinsa take, a haka har suka fara waec. Ta fito daga wanka knn bayan ta dawo daga 3rd paper dinta, tana tsaye gaban mirror tana goge dogon gashinta don karkashin shower tayi wankan kuma bata rufe gashin ba, vibration din waya taji ta koma gun gado ta dau wayar, d'agawa tayi ta kai kunne hade da langwabar da kai, daga daya bangaren yace "How was the paper?" tace "Uhm yayi sauki...." Yace "Upon the runs?" Wara ido tayi tace "No, ni ban Karba ba" yace "Alryt, me kike yi yanxu?" Tace "Wanka nayi...." Ya d'an yi shiru sannan yace "Ohk, kin ci abinci?" Ta girgixa kai tace "Nobody is at home, yanxu xan girka" yace "Me xa ki dafa?" Ta yi shiru kamar me naxari sannan tace "Kila in dafa indomie" yace "Uhm nima xan ci" ta xaro ido sai kuma tayi dariya tace "Indomie din?" Yace "Yeah, am very hungry, no body is at home here also" tace "Eyya, kuma baka iya girki ba koh?" Yace "Eh mana, but gashi xa ki yi mana ae" murmushi tayi tace "Da gaske zaka ci?" Yace "Ehh mana am jet serious..." Shiru ta d'an yi sai kuma tace "Ohk, toh wa xai karbar maka?" Yace "Oh baxa ki kawo min ba" shiru tayi sai kuma tace "A'a ka dai xo ka karba" yace "Toh shknn just leave it" tace "Ka fasa ci?" A takaice yace "Ehh" tace "Ohk toh" katse wayar yayi, tayi murmushi, ta karasa goge jikinta ta shafa lotion ta fito da abayar ta red and black ta sa, ta daure kanta da dankwali ta feshe turare ta fita, irish ta shiga ferewa cikin kankanin lkci ta gama ta soya, snn tayi sauce din hanta, tuni kamshi ya bade gidan ta xuba su a warmer ta tsaftace kitchen din ta fito, abincin ta dauka ta fita ta kulle gidan don tasan sae bayan isha mumy xata dawo daga service, tun fitowarta gate dinsu gabanta ke faduwa tunawa da su Ilham da tayi, amma cewa da yayi babu kowa gidan yasa hankalinta ya d'an kwanta, ba karamin karfin hali tayi na tura gate ba ta shiga bayan ta isa gidan, a hankali ta rufe gate din, ta nufi kofar parlor da sauri, ta murda kamar me tsoron handle din ta shiga snn ta rufe, kwance ta gansa kan doguwar kujera singlet da short nicker kadai ne jikinsa, k'in karasawa tayi ta ajiye abincin hannunta tana kirkiran murmushi tace "Uhm gashi na kawo ma, xan wuce...." Mikewa xaune yayi yana kallonta, can ya mike ya isa Inda take, ta sunkuyar da kai kamar munafuka, ya fi minti daya yana kallonta, snn a hankali ya kai hannu ya tsinke Rosary din wuyarta, ta dago da sauri mamaki dauke fuskarta tana kallonsa sai dai ta kasa cewa komai, ganin yanda ya tsareta da brown eyes dinsa still yasa ta sauke idonta a hankali, dago kanta yayi xae yi magana suna hada ido ya kasa cewa komai, da sauri ta sake sunkuyar da kanta ta juya xata bar wajen, ya jawota xuwa jikinsa murya can kasa yace "I....i missed you" kasa cewa komai tayi, ya hade fingers dinta da nasa hakan yasa ta dago a hankali, lumshe ido yayi ya daura warm lips dinsa a forehead dinta, da sauri ta rufe idonta, a hankali ya dinga gangarowa da bakinsa har kan hancinta sannan lips dinta, lkci daya ta rike breathe dinta, ya jinginar da ita jikin kofa ya lumshe ido ya hade bakinsu, bai saketa ba har sae da yayi me isarsa, ko ina na jikinta 6ari yake, yana xame bakinsa daga nata kuwa ta juya da sauri ta fice, bin bayanta yayi da rinannun idonsa ya datse gate din, hawaye ne ya cika idonta tana kallonsa tace "Ka bude min kofa" hannunta xai kama ta koma baya da sauri, xai matsa kusa da ita ta fasa wani ihu da yaji har tsakiyar kansa, bai san lkcn da ya bata hanya ta fita ba. Washegari Abuturrab na xaune parlon Abbansa, fuskarsa ba walwala yana sauraren yakumbo, can dai ya d'aga kai ya kalli Abba ya ga kallonsa yake, sauke kansa yayi, a fusace yakumbo tace "Ya xaka min shiru Ina maka magana Aliyu...." Ya gyara xama yace "Naji Umma, sai dai ni bana son auren xumunci...." Mikewa tayi tace "Ae ko ya xama dole ka so auren xumunci tunda ka kasa fidda mace ka aura.... Kayi xaton Umar so yake nuna maka da ya bar ka kake ta shashancin ka kaki ajiye iyali, ni ban taba ganin irin haka ba, wai xamani ya xo yanxu sai ka ga d'a namiji yana xaune gidan iyayensa yaki aure wae sae ana tilasta shi sai kace ba ribar sa bace, kai baka san gata ake maka ba koh?" A takaice yace "A bani yan kwanaki xan xabi matar aure, bani da ra'ayin na xumunci..." Tabe baki tayi tace "Ae shknn fitsararre, amma ka sani in dai bata da qualities din xama surkar mu wllh sai dai ka mutu, auren xumunci ba fashi..." Bai ce komai ba sai dai da ganinsa kasan he's boiling from inside, mikewa yayi ya dake yace "Toh shknn" tace "Ehe, kuma sati uku na baka...." Bai tanka ta ba yayi ficewarsa, ta kalli Abba tace "kasan me yasa nake son ganin Aliyu yayi aure Umar?" Abba ya kalleta yace "A'a yaya" ta koma ta xauna tace "Saboda 'yan adawar mu, masu maka gorin rashin 'ya 'ya maza, in sha Allahu sai Ali ya cika maka gida da jikoki maza....." Abba ya girgixa kai hade da murmshi bai ce komai ba sanin ba kowa take nufi ba banda 'yan ubansu...." Yakumbo yaya ce ga mahaifin Abuturrab don daga ita sai shi, kuma ta basa shekara daddaya har tara, su uku ne gun iyayensu, sai yan uba rututu, autarsu Maryam tana aure a Cairo, iyayensu gaba daya sun rasu tun kafin Maryam ta cika shekaru shidda yakumbo kuma tayi aure lkcn, bayan rasuwar mahaifansu ta maido da kannin nata gabanta duk da ba wani karfi gare mijinta ba a lkcn ga kuma 'ya yanta maza biyu sanin idan ta bar su gun kishiyar uwarsu wahala xa su sha, don hatta iyayensu ba wasu masu shi bane, ita kuma stepmum din tasu bbu laifi tana da abun hannunta don iyayenta suna da rufin asiri, ita kuma 'ya 'yanta takwas da kakansu Abuturrab, bata damu da 'ya yan mijin nata ba haka suka ta xama gidan yayarsu yakumbo (Fatima) har xuwa lkcn da kowa ya kama gabansa, 'ya yan yakumbo biyar duk maza sai autar ta Sumayya, manyan maxanta biyu duk sun yi aure, sae na ukun yanxu da take son a hada aurensa da na Abuturrab, Maryam kuma 'ya yanta uku, 'yan biyu maza sai autar ta khadija, sosai yakumbo tayi fafutuka kan makarantar Mahaifin Abuturrab don lkcn yana shekarsa ta biyu a jami'a Abbansu ya rasu don Mahaifiyarsu ta riga sa rasuwa, cikin ikon Allah Abban Abuturrab na gama karatun ya tafi NDA da taimakon mijin yayar tasa, bayan shekara daya ya samu aiki as a militant duk ta damesa sai da yayi aure, ya auri Mami (Hajarah) bafulatana kuma marainiya kamarsa, sun kuma hadu ne lkcn da yake service a Adamawa, bai shekara biyu da fara aiki ba Mami ta haifo masa d'an sa na fari Abuturrab a wnn shekaran kuma Allah yayi ma Mijin yakumbo rasuwa a hatsarin mota, sosai Abban Abuturrab yake kula da yayar tasa duk da 'ya yan ta duk sun riga sa fara aiki, promotions sosai ya dinga samu gun aiki sbda iliminsa da kwazo, sai gashi kafin shekara biyar ya xama babban soja Wanda hakan ya d'aga hankalin step members dinsu, Mami bata sake haihuwa ba sai Abuturrab na da shekara tara ta haifi Ramla a lkcn kuma Maryam ma ta haifi yan biyunta maza, autarta kuma sa'ar khaleesat ce, Yakumbo mace ce mai fada da isa ga masifa shi yasa ko kadan basa shiri da Abuturrab, kwata kwata bai son xuwanta gidansu, gashi duk abinda tace da Abba shi xae yi, baya taba tsallake magananta, iyakar biyayyar da xai ma mahaifiyarsu yake mata, a fusace ya shiga bedroom din Mami ta bi sa da ido har ya xauna, ganin ya ki cewa komai Mami tace "Ya aka yi?" Kamar xai mata kuka yace "Mami wai meyasa yakumbo take ma mutane haka ne, ni fa wllh tana cin darajar Abba da wataran sai munyi dauki ba dadi da ita...." Ta hararesa tace "Toh ka je yanxun ma kuyi mana tunda ka isa...." Marairaice mata yayi yace "Ba haka Mami ba ji fa wai maganan auren xumunci take min, kuma nasan kila tace da fitsararrun yaran yaya Khabir koh yaya Munnir xata hada ni, (Manyan mazan yakumbo)" Mami ta tabe baki tace "Wannan kuma kai ya dama.... Da baka tsaya ruwan ido ba ae da yanxu kayi auren ka, toh wai ina ya matan da kake bani a waya muke gaisawa?" Dariya yayi yace "Kai Mami ba wani ruwan ido fah, wa ennan kuma ae ba sonsu nake ba, kawayena ne kawai" ta tabe baki tace "Toh me kawaye, ae kuma sai kasan yanda xa ka yi" Mikewa yayi yace "Ke Mami baki taba neman min solution sai dai ki yi ta fito da faults dina, any way xan tafi gun Momma na anjima nasan she will surely find a way out for me" daga haka ya fita ta bisa da kallo tana murmushi. *Haske Writers asso*📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 14...... Daren ranan Abuturrab ya tafi gidan kanwar Maminsa Hajiya Mariya, tayi murnan ganinsa sosai bayan sun gaisa tace "Anya Abuturrab ba wajen wani ko wata ka xo a anguwar nan ba kayi branching din nn" Dariya yayi yace "Mumy wajen ki fa na xo da gaske" tace "Ikon Allah, to ka kyauta ya gida da su ilham?" Yace "Lafiya lau Mumy" tace "Toh yaya fa?" Yace "Ta ma ce a gaishe ki" Tace "ina amsawa, xan ma kira ta" Abinci ta xubo masa duk da yace ya koshi, haka dai ya dauka ya fara ci suna ta hira, jin gidan shiru yace "Bbu kowa Kenan gidan yau Mumy?" Tayi murmushi tace "Kasan an koma boko duk suna gun iyayensu..." Yace "Toh bari kawai in kwaso kayana in dawo taya ki xama tunda ilham ta guje ki" dariya tayi tace "Da ka kyauta mun Aliyu" shi ma yyi dariyar yace "Kar ki damu xan dawo Mumy" Hajiya Mariya bata taba haihuwa ba, sai dai 'ya 'yan mai gidanta kuma duk manya ne, sosai take da son yara, hakan yasa gidanta bai rabo da yara kanana ko da yaushe sai dai in sch period ne, ita ta raini ilham har tayi wayo tayi shekara goma a wajenta, daga baya yakumbo tasa Abba ya karbo ta ba tare da wani dalili ba. Karfe goma da kusan Rabi Abuturrab yace mata xai tafi, nan ta damu wae sai ya kwana, yace "Toh in har kina son in kwana Mumy sai in kin amince xa ki samo min solution din wata matsala da ta sha min kai" Mumy tace "Ae wnn abu me sauki ne son...." Murmushi yayi yace "to xan kwana...." Sai kusan sha biyu Abuturrab ya fadi ma Small mum din tasa damuwarsa, shiru tayi tana kallonsa, can tayi murmushi tace "Toh kai yanxu matar ce baka samu ba tukun ko ya?" Ya shafa kai bai ce komai ba, can yace "Ehh" tace "Ae ko akwai wata 'yar makwabciyar mu a nan layin yarinyar me kyau da ita, ga hankali ga ilimi ga nutsuwa, in dai Alhaji bai nan ita ke xuwa taya ni kwana, ni dai na yaba da hankalinta, yau ma kanwarsu na asibiti ne shi yasa baka ganta ba amma da tana nan yanxu haka" Tun da ta fara magana ya saki baki yana kallonta har ta kai karshe, tace "Ya na ji kayi shiru" hade rai yayi yana girgixa kai yace "Another solution plss...." Dariya tayi tace "Kai fa ba mutunci ne da kai ba Abuturrab" ya langwabar da kai yace "Ni dai bana son auren hadi Mumy samo wani solution" tace "To ka ce kai baka da wacce kake so fa" ya shafa sajensa a hankali yace "Mumy akwae wata da nake son halayenta, she's nyc, uhm I like her mum" ta gyara xama tace "Ikon Allah to ita a ina take?" Kamar baxai ce komai ba sai kuma yace "A unguwar mu" Mumy tace "Au abu me sauki, kayi ma Abba magana sai a tura gidansu mana" kamar bae gane abinda take nufi ba ya tsaya kallonta, tace "Kayi shiru kuma" lumshe ido yayi ya bude murya can ciki yace "She's a Christian Mum" xaro ido tayi tace "Christian kuma, ko dai ka ta6u ne Abuturrab, ana maganar arxiki ka sakko wannan..." Kamar xai yi kuka yace "Allah Mumy burgeni take..... I like her" ta hade rai tace "Kai bana son shashanci fa, me xai hadaka da arniya duk ilimin ka Aliyu" a hankali yace "A'a ba arniya bace Mumy, she have her religion, she's a Christian!" Da wani irin mamaki take kallonsa baki bude, tana girgixa kai tace "Ka fi karfina Aliyu, tashi ka tafi gidanku ka kwana, I don't think you are on ur right senses" saukowa kasa yayi yace "No Mumy, wllh nasan abinda nake, shawara fa na xo ki bani...." Da mamaki tace "Yau naga ikon Allah, wace shawara xan baka a kan kafura ni Mariya?" Shiru yayi yana kallonta, tayi tagumi tace "Yau ni nake ganin ikon Allah, are you okay Aliyu, Christian fa kace?" Sauke idonsa yayi daga kallonta yace "There's nothing wrong with this mum, ko an rufe shiga Islamic religion ne?" Kallonsa kawai take ta kasa cewa komai, murya can kasa yace "I can convert her Mum, baki son in samu wannan ladan..." Da damuwa tace "No son, meye makomar kids din ka, kar ka manta ita xa kayi converting ba family dinta ba, sannan Kasan baxa ta taba rabuwa da family dinta ba, Aliyu keep everything aside and think reality, this is the biggest mistake you are to make in ur life, that aside Kasan in dai yakumbo na da rai abinda baxae taba yiwuwa ba knn, ko Abbanka baxae yarda ba not to talk of ur mum bare a xo ga families wnn abun kunya ne Ali..... Ita yarinyar ance maka iyayenta xasu yarda su bar ta tayi converting?" Mikewa yayi a d'an fusace yace "Abun kunya don na auri wacce ta dawo addinin musulunci, toh ashe kuwa komai ma xae dawo abun kunya a duniya.... Mum nasan kin fi kowa tunani a parents dina, plss kiyi tunani ki ban shawarar da xae yi boosting din abinda nayi niyya, sannan in dai tana sona bbu ruwana da iyayenta, they can do what ever they wish to me" daga haka ya yi hanyar bedroom ta bi sa da kallo baki bude, kwanciya yayi kan gado ya lumshe ido, can ya bude da sauri ya dau wayarsa ya shiga kiran Samantha har ya gama ringing bata dauka ba ya kuma kira nan ma shiru sai yayi tunanin tayi bacci nan ko tana xaune tana karatun biology kawae ji tayi haushinsa take ji hakan yasa ko kallon wayar bata yi ba. Washegari Abuturrab na idar da Sallah yace xai tafi, Hajiya Mariya tace "Da wuri haka son, ka jira kayi breakfast mana" yace "Xan yi a gida" shiru tayi tana kallonsa, can tayi murmushi tace "Toh meye kuma na fushi son, ba fa mu gama magana ba" marairaice mata yyi yace "Bayan kin ki supporting dina Mum" tace "No ba haka bane son, am trying to highlight you of the side effect of what you are trying to do, na farko ur kidz, na biyu ur image, na uku your parent, na hudu her parent will and will never agree, na biyar makiyan ka will make jest of you....." Katse ta yayi yace "Mumy naga dai uba shi ke da iko kan 'ya ya ba uwa ba, image dina kuma will never be tarnished tunda ba mugun abu nayi ba, parent dina kuma naga ni xan xauna da abata fa Mumy, parent dinta kuma can do what ever they wish I don't care, snn ni bana hango dariyar da xa a min nafi hango ladan da xan samu gun Allah" lumshe ido tayi cikin sanyin murya tace "Haka ne, Allah ya dafa maka son, yayi xabi mafi alkhairi, ya kawo sassauci kan lamarin" Abuturrab da yaji dadin furucinta yace "Nagode Mum" Sai kusan Karfe goma Abuturrab ya bar gidan bayan ta basa shawarwari masu yawa. Har bayan kwana biyu bai ga Samantha ba gashi taki daukar kiransa, duk yaji Kamar an daura masa duniyar ne a kansa, da dadewa yasan ta daina bin inda tasan xai ganta, hakan yasa ya maida gun zamansa can gaban gate din main house dinsu, ae ko yana xaune gun ranan laraba ya hangota tana tahowa, bata lura da shi ba hakan yasa yayi saurin dauke kansa, yana ganin ta iso dai dai gate din ya mike sai a sannan ta gansa and she was very shocked, ta juya da sauri xata gudu taku daya biyu ya cafketa, tana xaro ido kamar munafuka tace "Doctor" janta yayi xuwa cikin gidan, sosai ta tsorata tana tirjewa tace "Plss ka bari mana, stop it plss, ur sisters...." bai saurareta ba har sai da suka shiga compound din, sojojin dake xaune suka bi su da kallo kamar idonsa xai yi magana, ko kallonsu Abuturrab bai yi ba, ita ko ta boye fuskarta jikinsa duk ta rikice hawaye na sakko mata, tsoronta daya kada yan gidan su gansu, bai tsaya ba sai da suka shiga parlonsa ya saka key ya jingina jikin kofar yana kallonta, kin yarda ta kallesa tayi ta hade rai tace "Let me out" fixota yayi ya hade ta da bango yace "Why ain't you picking my call?" Kasa cewa komai tayi tana kallonsa can kasar xuciyarta na bugawa ganin yanda ya hade rai, can ta sunkuyar da kai ya kuma dago Kanta, hawaye ya cika eye balls dinta tace "Ni ka bude min kofa in fita" shiru yyi yana kallonta, can ya sa hannu ya tsinka rosary din wuyarta da cross, xaro ido tayi ta rike tsinkakken rosary din a fusace tace "Meyasa xaka dinga tsinkar min da rosaries....." Yana kallon kwayar idonta yace "Coz I don't see it use on ur neck, it's of no use..." Kallonsa take ta kasa cewa komai, yace "Why are you ignoring my calls?" Rungume hannayenta tayi tace "I see you are good at kissing girls, and my religion prohibit that, because it's almost an act of fornication that's why I decided to quit the frndship....." kallonta yake ko kiftawa bai yi, can ya fixgota yace "Fornication? Kin san meye fornication?" Tsorata tayi ganin yanda ya rike ta amma ta dake ta tura sa tace "Let me out" k'in saketa yyi yana mata wani kallo yace "Sae kin gaya min the meaning of Fornication" Hararansa tayi tace "You check the dictionary" Dago kanta yayi yana mata wani kallo yace "Have i ever attempted having sex with you?" Kauda kanta tayi ta hade rai bata ce komai ba, yace "Alryt then, but you can't just call me a fornicator without me having sex with you, don haka let me make it happen sai ki ji ddin kirana da haka...." *Haske writers asso*📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 15..... Dago kanta yyi yace "Have I ever attempted having sex with you?" Kauda kanta tayi ta hade rai bata ce komai ba, yace "Alryt then, but you can't just call me a fornicator without me having sex with you, don haka let me make it happen sai ki ji ddin kirana da haka...." Daga haka ya kama hannunta xuwa bedroom, sosai ta tsorata ta dinga turasa tana tirjewa hade da cewa "Ni ka bude min kofa in fita, let me out immediately...." Daukarta yayi cak ta kankamesa a rikice tana cewa "plsss let me out.." Bai tsaya ba sai da ya shiga bedroom ya rufe kofar da key ya direta kan gado, da yake shidda na yamma ya kusa bedroom din yyi duhu don duk curtains a sauke suke, rigar sa ya cire yana kallonta, ta mike da sauri ya kuma mayar da ita ta fasa ihu ya hau gadon ya rufe bakinta, ya cire dankwalin kanta, gashinta me yawa na daure tayi dough da shi, ta cire hannunsa a bakinta cike da tashin hankali tace "Don Allah kayi hakuri ka rufa min asiri" ya kai bakinsa kunnenta yace "You called me an adulterer???" Ta fashe da kuka tace "Noo amm sorryyy.... I didn't mean it" Hannu ya kai bayanta a hankali ya xuge zip din doguwar rigar jikinta hade da 6alle bra dinta, rikicewa tayi ta rike hannunsa cikin kuka tace "Pls let me, ka yi hakuri pls..." Yana kkrin cire rigar yace "After all you are not a virgin" xaro ido tayi tace "I swear ni ba yar iska bace" fixgota yayi lkci daya idonsa ya kada yace "Ke ba yar iska bace? Salahai ne ke xuwa Club dama?" Kasa ce masa komai tayi hawaye na sakko mata har da sheshsheka, lkci daya ya sauke rigar gaba daya har xuwa waist dinta, kankamesa tayi ko ina na jikinta na rawa tace "Don Allah ka rufa min asiri, ni ban taba ba....." Lumshe ido yayi jin bare body dinta a jikinsa, ya kai bakinsa wuyarta cikin sanyayyan murya yace "I won't, because i... I love you" jin tayi shiru ya dago kanta a hankali, da sauri ta rufe idonta, ya kai lips dinsa kan eyelid dinta snn a hankali ya xuge mata zip dinta, sauka take son yi daga kan gadon ya rikota taki barin su hada ido ya maido ta kan gadon yace "I promise I won't kiss you again tunda ba kya so, don't ever ignore me again plss, missed you" sai a sannan ta dago manyan idonta ta kallesa, ya langwabar da kai yace "Pls dear" sauke idonta tayi kasa, ya dau ribbon dinta da ya fadi ya tufke mata gashinta snn ya dau dankwalinta ya mika mata, a hankali ta sa hannu ta karba, mikewa yayi ya kunna bulb din dakin, ya koma kusa da ita ya kamo hannunta yana murmushi yace " _Girl I have a question to ask you today....._" Dago kai tayi ta kallesa ya wara mata ido yana murza long fingers dinta yace " _Will you marry me even though I met you today_" kallonsa ta tsaya yi ko kiftawa babu, yayi murmushi ya daura forehead dinsa a nata cikin sanyin murya yace " _All she said... You don't even know my father, o de mo mi rara.... You don't know my mother, ofe fi mi s'aya, can you pay my pride price it's just a million dollar! Easy o jeje take it slow oh, ko le to yen my darling jeje, easy o jeje take it slow oh, omo la fe fe ra moto, easy o jeje take it slow oh, will you take it easy I dey on prada.... Easy o jeje take it slow oh...._" Xaro ido tayi tana kallonsa, ya wara ido yana kallonta, tace "kana jin Yoruba dama?" Murmushi yayi yace let me finish, ta tallabi chin dinta tace "Ohk ohk" jingina yayi jikinta hade da lumshe ido yace " _Girl I have just one thing to tell you again, is it me or this love lo yan me were, ahh! I don't even know ur father, mi ode mo ile won oh.... I don't know your mother mo de fe fi e s'aya, can't pay ur price oh, don't even have one dollar ah.... Easy o jeje take it slow oh, ko le to yen my darling jeje, easy o jeje take it slow, omo la fe fe ra moto, easy o jeje take it slow, will you take it easy I dey on prada.... Easy o jeje take it slow ohh...._" Murmushi tayi ta mike ya riko hannunta yace "No comment" tace "Ohk kayi kokari...." Bata fuska yayi yace "I mean you did not reply my song" ta buda ido tace "Buh I said it's nyc...." Yace "Uhm it came from the bottom of my heart..." Tace "na tafi" daga haka ta nufi kofa yace "Ohk, I won't kiss you again plss, don't quite the frnd ship" ta kallesa tace "Sure?" Mikewa yayi tana ganin haka ta karasa kofa da gudu ta murda taji a rufe, jawota yayi jikinsa ta baya yace "Yeah sure!" Kasa cewa komai tayi don ji tayi kamar da electric ya hade jikinta, bude kofar yayi yace "Ina za ki?" Kin cewa komai tayi, ya juyo da ita suna facing juna, yana kallon kwayar idonta yace "Ina za ki nace?" Sauke idonta tayi a hankali tace "Mumy ta aikeni gidan frnd dinta...." Yace "Let me drop you" tace "A'a an fara kiran sllh" kama hannunta yayi suka fita parlor, ya dau makullin motarsa ya ja ta xuwa gun mota, gidan bbu wani nisa tace ya ajiyeta d'an nesa da gate din, hakan yyi yace tayi sauri yana jiranta, kai kawai ta gyada masa ya bi ta da kallo har ta shiga gidan. Ba a dau lkci ba ta fito ya bude mata motar ta shiga, kallonsa tayi cikin sanyin murya yace "Welcm...." Jan motar yayi ya dau hanyar gidansu, yace "Kun gama waec din ne?" Ta girgixa kai tace "Mun kusa." Bata bari ya tsaya kusa da gidansu ba yana parking ta bude motar ta fice hade da daga masa hannu, murmushi yayi ta juya ta nufi gate dinsu. Washegari sai gashi ta biyo hanyar xata Church, fita yake da niyar yi xuwa gun wanin abokinsa amma ba da mota ba, yana ganinta ya fasa, ita ko ta gaishesa xata wuce ya sha gabanta yace "Ina za ki?" Tace "Church" ya d'an tabe baki yace "During waec din ma baxa ki tsaya kiyi karatu ba?" Tace "Mumy ce tace sai naje, beside nayi karatu tun safe" ya d'an bata fuska yace "ohk but am very hungry, nobody at home to give me food" *Haske writers asso*📚✍🏻 I heart you all my fans😍😍 💫 *Noorul Huda*💫 16..... Yar dariya tayi tace "Then ka tafi eatry mana!" Yace "No, not when I have a sweet girl that's very good cook!" Ta xaro ido tace "Who?" Yace "Youu" daga haka ya kama hannunta ya ja ta zuwa gidan, tana bata rai haka ta shiga daura masa girkin garnished spaghetti, cikin mintinan da basu wuce ashirin ba ta gama suka dawo parlor, duk yanda ya so da ita ta ci kin ci tayi shi kuma ya kulle kofa ya ki barin ta ta fita, ganin yanda ta hade rai yayi murmushi yana cin spagh dinsa yace "Tell me a story...." Bata ko kallesa ba tace "Bn iya ba" jawota yayi kusa da shi yace "Baxa ki bar gidan nn ba knn yau" kin cewa komai tayi, ya lumshe ido ya bude yace "Ohk tell me more about Jesus!" Kallonsa tayi da sauri sai kuma tace "Tarihinsa?" Ya gyada mata kai, gyara xama tayi tana kallonsa tace "Ohk I will" Yace "Yauwa am all ears" ta rufe ido tace "Long time ago in Bethlehem, so the holy bible said, Mary's boy child Jesus Christ was born on Christmas day, even the angels testified that a king was born...." Murmushi yyi yace "No.... da Hausa xa ki min and you are not giving me in details, how was he born, where was he born, da dai sauransu" ta wara ido tace "Ohk Ohk... Mary wacce kuke kira da Maryam ita ce mahaifiyarsa, Mary macece baiwar Allah me kamun kai kowa a Bethlehem ya shaida hakan, tana kuma da wanda xata aura wato Joseph wanda ya kasance Carpenter, ranan tana xaune ita kadai daki sai ta ga wani haske daga waje, haske sosai wanda sai da ta rufe idanuwanta, Mala'ika Gabriel kenan ya xo mata da sakon cewar xata haihu ba tare da aure ba, abun ya bata mamaki sosai, kafin tace komai har ya bace nan ta fara naxari sai dai bata fadi ma kowa ba har Joseph da xata aura, wasa wasa taga da gaske ciki gareta, wanda hakan yasa 'yan gari suka fara maganganu kanta, ko ina gulmarta ake wasu na cewa da ma lullubin karya take a ko da yaushe, tayi kkrin ganar da su cewar ita bata taba sanin namiji ba amma nobody was willing to believe her, sae Joseph da bai gujeta ba, bayan an dau lkci xaman kasar ya gagaresu sbda mutane wanda hakan yasa Joseph yasa su bar garin, a hanya nakuda ya kamata Joseph ya shigar da ita gun ajiye dawakai wato horse stable a nan ta haifi Jesus Christ the son of God!" Abuturrab dake ta kallonta cike da tausayi ya dakatar da ita da sauri jin furucin ta na karshe yace "Madam He's not the son of God but rather his messenger" kallonsa ta tsaya yi sae kuma tayi murmushi tace "Yeah, believe din Muslims knn, but we believe he's the son of God" hade rai yayi yace "Ina gaya maki magana kina ce min ba haka ba, Allah bai haifa ba ba a haifesa ba, he's one and one alone, Jesus is his messenger!" Shiru tayi tana kallonsa can ta girgixa kai tace "For God so love the world, that he gave his only begotten son that who so ever believeth in him shall not perish but have everlasting life, this is a verse from the holy bible don me xaka ce jesus isn't the son of God?" Wani kallo ya dinga mata can yace "Then ur bible is deceiving you" hade rai tayi sosai tace "How dare you? why will you say that?" Mikewa take son yi a fusace ya fixgota ya xaunar da ita yace "Luke 3:38 said; Adam was the son of God, Gen 6:2 also said all men are son of God, Jeremiah 31:9 said David is the begotten son of God, Psalm 2:7 said who ever ia righteous is the son of God, Romans 8:14 says Jesus is the ONLY begotten son of God, which are we to believe?? There is a lot of confusion in ur bible, nan ance mana Jesus kadae ne son of God, an dawo an lissafo mutane da dama an kirasu da son's of God su ma, why? How's that??? Ashe kenan ba Jesus kadai ne son of God din ba ma," Kallonsa take ko kiftawa babu, ya tabe baki yace "Ci gaba" Sauke idonta tayi a hankali tace "Am going home" daga haka ta fara kokarin mikewa yace "Baki isa ba you are not leaving here until u finish ur forged story" wani kallo tayi masa sai kuma ta fashe da kuka tace "It's not forged" tabe baki yayi yace "Then ki ci gaba since you didn't defend my question" ta goge hawayen idonta a hankali tace "Three wise men ne suka yi announcing haihuwar Jesus the Messiah..... Snn comet from the sky ne yayi leading dinsu har manger inda aka haifi Christ....." Dakatar da ita yyi yace "Yeah yeah... jump all this...." Cikin sanyin murya tace "Allah ya ba ma Christ baiwa da dama yana kuma da disciples 12 wato mabiya har sha biyu, first miracle din da jesus yayi on earth shine na tada matattace, Lazarus ya mutu yan uwansa na ta koke koke Jesus ya je tomb dinsa ya tado sa ya fara rayuwa kuma, ya warkar da mutane dayawa don ya kasance mutum me tausayi, akwai wani biki da suka je da mahaifiyarsa Mary, wine ya kare gun bikin, nan Mary ta nemosa tana tambayarsa ya xa ayi, nan yasa aka ciccika masa ruwa a pots ya maida su wine gaba daya, shine kadai mutum da ya taba tafiya a kan ruwa da kafafuwansa, ya taba ciyar da dubban mutane da bread guda biyar da kifi biyar yayi miracle suka cika baskets fiye da dari.... John the Baptist shi yyi baptizing Jesus....." Jin ana kiran sllh la'asar ya dakatar da ita yace "Alryt xan je sllh idan na dawo sae ki karasa, nima kuma sai in baki nawa tarihin islamically then you compare and contrast" a hankali tace "Ohk...." Rufe sauran abincin da ya rage yayi, tace "Ka koshi?" Bai tanka ta ba bai kuma kalleta ba, bayan yan mintuna ta mike xata wuce ya mayar da ita ya zaunar, hade rai tayi tace "Wucewa xan yi" bai ce komai ba kuma bai saketa ba, bayan wasu minutes din ya saketa yana kallonta yace "Idan ana kiran sllh ba a magana" buda ido tayi tace "da gaske?" Mikewa yayi yace "Yesss" mikewa tayi ita ma yace "Baxa ki jira in dawo ba kuma?" Hade rai tayi tace "Kai xaka sllh, ni kuma baxan je church ba, me yasa kai ma baka fasa xuwa sllhn ba" kallonta kawai yake, can ya juya yayi ficewarsa, kamar xata yi kuka ta bi sa da kallo, samun kanta tayi da kasa fita, a hankali ta koma ta xauna. Sosai yayi mamakin ganinta da ya dawo daga masallaci amma bai nuna ba, ya xauna kusa da ita yace "Oya karasa in fara nawa!" Ta sauke idonta ta ci gaba da basa tarihin, tun daga kalubalen da jesus ya fara samu gun nonbelievers, da encounter dinsa da paul the apostle, da yanda paul ya dawo Christianity, irin sharrin da nonbelievers suka yi masa, da last dinner dinsa da disciples dinsa, da yanda soldiers suka xo suka yi arresting dinsa, aka saka masa crown din k'aya a kai, aka ja sa tare da cross dinsa xuwa Golgotha ana cin xarafinsa, da yanda aka saka shi tsakanin barayi biyu, yanda aka daura sa cross din aka buga masa kutsoshi a hannu kallonta Abuturrab yake da mamaki ganin hawaye idonta, ya danne dariyarsa yana kallonta da tausayin rashin sani wanda aka ce ya fi dare duhu, cikin sanyin murya tace "Jesus Wept!!! And his last words where; Ohh father, forgive them because they don't know what they are doing!" and that was how jesus Christ died for our sins, he was crucified on the cross in Calvary, he was slain" ta karashe tana goge hawayen idonta, yana mata wani kallo yace "Ohh da gaske ya mutu ashe? Kuma sbda xunuban mu? he died on the cross for all our sins?" Ta kallesa tace "Yess! But he rose up after 3 dayz and his father took him to heaven...." Da mamaki yace "But.... But Why then do we still have to go to hell and pay for them again, don me wasun mu xa su je wuta bayan sbda xunuban mu ya mutu? Wato sau biyu kenan xa ayi judge dinmu.... Toh sacrifice din da jesus yayi sbda xunuban mu bai isa ba knn har sae an sake mana hukunci? Ina ce don xunuban mu ya yarda ya mutu, to in haka ne kenan he did not die for our sins tunda har hukunci pa na jiranmu ranan gobe kiyama, idan kuma ba haka ba ki fahimtar da ni yanda xan gane, kuma ni dai nasan it wasn't Jesus Pbuh that was Crucified or slain.... Another error from your Bible" yana kai wa nan ya wani hade rai wanda hakan yasa ta kasa cewa komai tana kallonsa ko kiftawa bbu, ya wara ido yace "Kinyi shiru?" Ta dauke kanta, ya kamo hannunta yace "Ki ganar da ni mana Samha" ta xame hannunta a hankali tace "I don't know too, all my Bible told me was that he died on the cross and rose from his tomb after 3 dayz and was taken to heaven bayan wannan ban san komai ba" innocently tayi maganan, murmushi yayi yace "Toh shknn, are you ready in fara baki nawa tarihin?" Bata ce komai ba ta sauke idonta kasa, ya lumshe ido yace "Alryt, His mother is Maryam Bint Imran, the daughter of Hannah......" Shiru yayi yana kallonta, ta d'ago a hankali jin shirun, murya can kasa tace "Ci gaba" yayi murmushi yace "Ohk...." *Haske Writers asso*📚✍🏻 Astaghfirullaahal Adheemal lathee la ilaaha illaa huwal hayyul qayyumu, wa atoobu ilayhi!! Allah knows best. 💫 *Noorul Huda*💫 17..... Maryam bint Imran shi ne sunanta, mahaifiyarta kuma Hannah, an san Maryam a mace mai son ibada da tsoron Allah a Jerusalem, Mala'ika Jibril shi ya xo mata da wahayin haihuwar Isa Pbuh, da farko taji tsoron ganinsa ta kuma nemi tsarin Allah daga gare shi, and he told her he was only a messenger from Allah, yana kuma yi mata albishir da kyautar A righteous son from Allah, Maryam tayi mamaki da jin hakan don tasan bata da aure kuma ita budurwa ce, a nan tace "Amma taya hakan xae yiwu..." Nan mala'ika jibril yace mata hakan xa'ayi domin Allah yana halittan abinda yaga dama, when he decrees a matter he only says to it 'Be' and it is. (Qur'an 3:47) and that was how Maryam (As) submitted to the will of Allah SWT and secluded her self from society and gave birth to Isa (AS) right under a Date palm tree (Bishiyar dabino) which serve as her source of Nourishment during labour not in a manger as said in your Bible." Murmushi Samantha tayi bata ce komai ba, Yayi murmushin shi ma ya ci gaba, "Maryam ta koma gun 'yan uwanta da Isa pbuh a hannunta, wanda hakan yasa aka fara condemning nata a garin a cewarsu ta aikata sa6o, ko kadan Maryam bata girgixa da surutansu ba tana rike da Annabi isa a cot dinsa, Allah SWT bai barta a haka ba don a nan take isa AS ya bude baki yace "Lallai ni bawan Allah ne...." Shiru yayi ganin yanda ta bude idanuwa tana kallonsa, yace "Ya?" A hankali tace "Uhm ci gaba..." Murmushi yayi ya langwabar da kai yace "He continued saying, Allah has made him blessed wheresoever he be, he has enjoined on him prayer and alms as long as he live, and to be dutiful to his mother, and Allah has made him not arrogant, unblest, and peace be upon him the day he was born, and the day he will die, and the day he shall be raised.... Qur'an 19:30-34." A tare suka kalli kofa da sauri jin an bude, Ilham tayi tsaye bakin kofar tana kallonsu, mikewa yayi fuska daure yace "You re very stupid, baki da hankali xa ki shigo min parlor haka??" Fita tayi kamar xata yi kuka tace "Kayi hakuri yaya Mami ce tace in kira ka..." Yace "Get out!" Rufe kofar tayi ta wuce, Samantha da duk jikinta yayi sanyi ta kallesa tace "Saboda ni kayi mata haka?" Xaunawa yayi kan kujera fuska daure yace "No" ta mike cikin sanyin murya tace "Ohk xan tafi" tashi yayi da sauri yace "No but ae ba mu gama ba Samha" tace "Xa mu ci gaba next time, kaga ur mum is calling" d'an murmushi yayi yace "Alryt... Thanks for the food dear" murmushin ta mayar masa ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita, komawa yayi ya xauna ya jinginar da kansa jikin kujera hade da lumshe ido, yafi minti goma a haka can ya mike jiki a sanyaye ya fita xuwa main house, sosai gabansa ya fadi ganin yakumbo, sae dae ya fuske ya xauna ya gaisheta tace "Sae yanxu ka ga dama kenan" ya shafa kai yace "A'a" Mami dae sae kallonsa take, Yakumbo tace "Toh ya maganar mu ta ranan, kasan dae kai ake jira ko?" Ta gefen ido ya kalleta yace "Ni ake jira kuma?" Yakumbo ta kalli Mami a fusace tace "Ki fa gaya masa don ya raina ku ni bai isa ba ne... Ni xae dinga ma tambayar walakanci?" Abuturrab yace "No ban gane xancen bane yakumbo." Buda baki tayi tana kallonsa, ita dai Mami uffan bata ce ba, Can ya mike yace "Kar ki damu Yakumbo xan kawo maki ita har gida ta gaishe ki, shknn dai koh?" Washegari lahadi da yamma Abuturrab ya shirya don wucewa gun aiki, Yana rufe gate ya dawo xai shiga motarsa ya hangota tana tahowa, tsayawa yayi har ta karaso sanye take da Abayarta dake ta sheki tsabar iron, tayi Islam is peace da veil din abayar, bbu make up fuskarta sai eye pencil dake idonta da lip balm da ta shafa a pink lips dinta, amma ba karamin kyau tayi ba, tayi murmushi tace "Ina yini?" Yana kallonta yace "Lafiya! Ina xa ki?" Tace "Catechism yau Sunday!" Yace "Ohk shigo in yi dropping din ki" tace "Thought clinic xaka?" Yace "Yeah" ta langwabar da kai tace "Toh ae ba hanyar bane" yace "Idan xa ki shigo malama ki shigo" a hankali ta karasa ta bude motar ta shiga, shi ma ya shiga ya ja motar suka dau hanyar titi, ganin hanyar da ya dauka ta kallesa sai dai bata ce komai ba, tafiyar kusan minti ashirin suka yi ganin har sun wuce hanyar asibitin ta kallesa tace "Ina xaka kai ni Doctor?" Ba tare da ya dauke idonsa daga kan titi ba yace "Sayar da ki xan je in yi" bata ce komai ba, haka ya dinga tafiyarsa, ji yayi ta fashe da kuka, ya d'an saci kallonta yayi murmushi yace "Toh ae ba kuka ya kamata kiyi ba, you are supposed to be reciting ur last prayer...." Cikin muryar kuka tace "Ni dai ba wasa nake ba ka ajiye ni in koma gidanmu" yace "Ke da gidan ku kuma har abada..." Ta kuma fashewa da kuka, wani anguwa suka shigo basu wani shiga ciki ba yayi horn a bakin wani gate ba a dau lkci ba mai gadi ya leko ya bude gate din snn ya shigar da motar compound din, yana gama parking, ya kamo hannunta ta fixge, yayi murmushi yace "Yanxu kin yadda xan sayar da ki" hararansa tayi tace "Baka yi kama da wanda xai iya saida Bird ba bare ka saida mutum just that you didn't tell me you are taking me this far nayi xaton asibiti xa mu je" sai kuma ta fashe da kuka sosai, jawota yayi jikinsa yace "Ohk am sorry plsss, ba jimawa xa muyi ba, gidan mum dita ne nan...." Turasa tayi da mamaki tana kallonsa tace "Mum?" Yace "Yeah, my mum sister" ta fashe da wani sabon kukan tace "Ni dai ba ruwana ka kai ni titi in hau tricycle in koma gida" yace "Ohh she's nyc, and she will love seeing you, bata da matsala" bai jira cewarta ba ya ciro handki ya fara share mata hawayen idonta, daga haka ya bude motar ya fita ya xaga ya bude mata kofar ya fito da ita. Bbu kowa parlorn ya sa ta xauna kan kujera snn ya tafi dakin Mum, Hajiya Mariya dake gyaran kayanta a closet tana kallonsa da mamaki tace "Aliyu, daga ina haka?" Yace "Gida Mum" tace "Ikon Allah, sannu da xuwa ya hanya?" Yace "Alhmdllh, da bakuwa muke" bai jira cewarta ba ya fita, sai ga ta ta biyosa, tun bata iso parlon ba take kallon Samantha har ta iso, Samantha ta sunkuyar da kanta gabanta na faduwa, Murmushi dauke fuskar Hajiya Mariya tace "Sannu da xuwa bakuwa" Samantha bata iya ta kalleta ba ta xamo kasa a hankali tace "Ina yini Mumy" Hajiya Mariya tace "Lafiya lau, ya hanya?" Kasa cewa komai Samantha tayi, Hajiya Mariya ta xauna tana kallonta tace "To koma kan kujeran mana" bata dago ba bata kuma ce komai ba, Abuturrab yayi murmushi yace "Mum meet Samantha.... But I do call her Samha.." Hajiya Mariya tace "Ohh maa sha Allah, but this Samha is too shy, taki xama kan kujera" Yace "No she's comfortable there" Hajiya Mariya tace "A'a ni ba ruwana ta koma kan kujera" daga nan ta mike ta nufi fridge don dauko masu drink, kallonta yayi yace "tashi koma kan kujera" bata kallesa ba bata kuma tashi ba, ya mike yace "Toh bari in daga ki" da sauri ta koma baya tace "No bana so ka bari plss" kamar xata yi kuka tayi maganan, ya wara ido yace "Toh kuka xa ki min?" Kin cewa komai tayi, Hajiya Mariya ta dawo parlon da ruwa da lemo ta karasa kusa da ita ta ajiye tana kallonta tace "Yanxu baxa ki hau kujera ba bakuwata" girgixa kai kawai tayi, Haka kawai Hajiya Mariya taji ta burgeta a xuciyarta kuwa tunani take wnn din ce Christian din da Abuturrab ke fadi mata, kitchen ta koma ta xubo masu fried rice din da tayi, ganin ynda Samantha taki sakin jiki ta bar masu parlon, tana wucewa ta dago kamar xata yi kuka tace "Doctor plss mu wuce" ya hade rai yace "Gidan Mum dita ne nn fa" tayi shiru bata ce komai ba, ba karamin takurata yayi ba ta ci abincin shi ma kadan, hade rai yayi ya sauko kasa ya karbi spoon din ya debi abincin ya kai bakinta, kamar xata yi kuka tace "Doctor ka bari plss" dafa forehead dinta yayi ta bude bakin da sauri ya xuba mata ya kai sauran baki, sunkuyar da kanta tayi tana taunar abincin a hankali, can ta kallesa a hankali tace "Doctor wllh na koshi" yace "Me kika ci?" Tace "Pounded yam and vegetable" yace "Shine baki kawo min ba?" Ta wara ido tace "Kana so?" Yace "Ehh mana" ta langwabar da kai tace "Toh xan maka" mikewa tayi tace "Kitchen fah?" Ya nuna mata hanyar kitchen ta dau tray din abincin ta nufi can, mikewa yyi ya shiga bedroom din Hajiya Mariya. Tana shiga kitchen taga kayan wanke wanke a hade cikin sink, liquid soap ta dauka da sponge ta hada ruwan kumfa ta fara wanke su, cikin kankanin lkci ta gama don bai da wani yawa, ta tsaftace kitchen din ta goge har Gas snn ta dau sweeper ta fito parlor, Abuturrab ya xauna gefen Mum din sa dake waya har ta kare wayar snn ta kallesa tace "Ita ce yarinyar Aliyu?" Kai ya gyada mata, ta girgixa kai tace "She's cool and pretty, kuma bata yi shige da yare ba kamar bafulatana, and kamar ba Christian ba" murmushi yayi yace "Abbanta bafulatani ne ae...." Shiru Hajiya Mariya tayi, can tace "Allah sarki.... Toh yanxu ta yarda xata yi converting din ne?" Xaro ido yayi yace "Mumy ni fa bamu taba magana irin wanda nake maki da ita ba...." Da mamaki tace "Kana nufin bata san kana sonta ba?" Shiru yyi sai kuma ya girgixa kai a hankali yace "Ko ma ta sani bata taba nuna ta sani ba" Hajiya Mariya tace "Toh fah, then it's better ka fadi mata soon as possible kaji ra'ayinta" ya lumshe ido yace "Ohk mum" 'yan shawarwari ta basa sannan tace ya tafi parlor ya bar ta ita kadai, mikewa yayi ya fita, xaune ya sameta idonta na kan tv, ya karaso ya xauna kusa da ita yana kallonta yace "Sae bayan magrib xa mu tafi koh?" Ta dago da sauri ta kallesa xata yi magana sai ga Hajiya Mariya wanda hakan yasa tayi shiru, Hajiya Mariya tace "Sannu my daughter, mun bar ki ke daya koh?" Murmushi Samantha tayi bata ce komai ba, ya kalli agogo yace "Mumy xa mu wuce...." Tace "So early?" Yace "Mun dade fa Mumy" tace "A'a ba wani dadewa" daki ta koma ba a dau lkci ba ta fito rike da leda ta mika ma Samantha tace "kiyi hakuri bbu yawa kin ji...." Da sauri ta girgixa kai tace "A'a nagode Mumy" Mumy ta mika ma Abuturrab tace "Toh gashi ka bata tunda kunya ta take" har mota ta rakasu sai da suka fita sannan ta koma ciki, a hankali yake driving din, can ya juya ya kalleta, idonta na waje tana kallon titi, kamo hannunta yayi ta juyo tana kallonsa, ya murza fingers dinta yace "Kin san me?" Janye hannunta take son yi ya ki saketa, murya can kasa yace "My mum.... Kinsan me tace?" Kallonsa ta sake yi snn tace "A'a" murmushi yayi murya can kasa tace "Wai tana son ki, she likes you, how she wish you were a Muslim sai ki xama in-law dinta" murmushi tayi ta kwace hannunta bata ce komai ba, yace "Kin yi shiru" wara ido tayi tace "Uhm and unfortunately am not a Muslim" *Haske Writers Asso*📚✍🏻 sorry for the delay! 💫 *Noorul Huda*💫 18..... Murya can kasa yace "And you can't become one koh?" Wani kallo tayi masa ta gefen ido tace "as in?" Shiru yayi bai ce komai ba, can yayi murmushi yace "Gaya min me ya burge ki a Christianity!" Ta girgixa kai tace "I don't want to talk about that now!" Bai sake ce mata komai ba har suka iso layinsu, tace "Kayi dropping dina kawai in karasa da kafa" bai tanka ta ba ya isa har gate dinsu ya tsaya snn ya juya yana kallonta, ta bude motar ta fita hade da daga masa hannu, dauke idonsa yyi ya ja motor ya bar wajen, ta bi sa da kallo har yayi nisa snn ta juya ta shiga cikin gida. Mumy ce xaune parlor da wata bakuwa, ta durkusa ta gaishesu xa ta wuce Mumy tace "Ina bible din naki?" Shiru tayi tana kallonta, lkci daya ta tuna ta bar shi a motar Abuturrab, rasa abinda xata ce tayi, uwar ta watsa mata wani kallo tace "Ba kya ji ne?" Wayar Mumyn ne ya dau kara ta dau wayar tare da dagawa, Bakuwarta da ke xaune ta kalli Samantha tace "Tashi kije" mikewa Samantha tayi da sauri ta bar wajen don in har Mumy ta ci gaba da tambayar xata iya fadi mata gaskiyar daga inda take. Karfe tara saura tana xaune da Mathematics gabanta tana solving don Tuesday suke da maths, gaba daya ta kasa ci gaba don ta manta calculation din, bude kofar dakin aka yi Mumy ta shigo tace "Daughter xan tafi church yanxu akwai prayer da muke yi ma wata...." Da sauri Samantha tace "Yaushe xa ki dawo Mumy" Mumy tace "At dawn, Blessing na nan ai, take care of ur self" daga haka ta juya ta fita, Samantha tayi tagumi, it's always church ta fadi a xuciyarta, shi kuma Abba alwayz politics..... Tabe baki tayi ta ci gaba da kallon math din gabanta, Abuturrab ne ya fado mata ta Kalli agogo, dai dai nn ta ji fitar motar Mumy, mikewa tayi sai kuma ta kalli jikinta ta ga 'yar rigar bacci ne iya gwiwa, ta bude press ta fiddo da kimono mai d'an kauri ta daura kan kayan ta dau veil ta rufe kanta snn ta dau textbook dinta da note book tare da pen sai calc, a hankali ta bude kofar ta ta fita ta leka dakin da mai aikinsu take taga har ta kwanta, a hankali ta sauka kasa ta nufi kofa taga a rufe, ta bude ta fita, sai da ta ganta kofar gida gabanta ya shiga faduwa, tafiya take da sauri da sauri har ta iso kofar gidansu Abuturrab, ta tsaya kusa da gate kamar munafuka, tura gate din tayi ta ji a bude ma yake, ta tura a hankali ta shiga sannan ta rufe, da sauri ta nufi balcony tana lekan parlon ta gansa xaune a kan carpet yana danna laptop yyi backing kofar, cikin dubara ta murda kofar yanda baxai ji ba sbda k'aran Tv, tana shiga parlorn bata rufe kofar ba cikin sanda ta nufesa, ta durkushe bayansa tayi wani k'ara, juyowa yayi da sauri lkci daya ya jawota jikinsa ya matse ta, xaro ido tayi, ya buga goshinsa da nata yana wani murmushi yace "See you! Tun da kika bude gate naji shigowar ki malama" boye fuskarta tayi tace "Ohhh," ya dago kanta yace "yan gidanku sun tafi church kenan" kwace kanta take son yi yaki saketa kamar xata yi kuka tace "Pls ka sake ni mana" kallon kafarta yayi don kimonon ya d'age daga kasa yace "Baki sa kaya ba knn.." Bai kai karshe ba ya dage kimonon, sai ga long legs dinta a waje, ta wani hade rai tana kkrin kwace kanta tace "What's this" ya buda ido yace "Ohh sorry, i never knew you were naked" wani kallo ta watsa masa tace "Am not naked" ya fashe da dariya, ta samu ta kwace kanta ta mike ta dau litattafenta ta nufi kofa, ya tashi da sauri ya isa gun kofar ya rufe, kallonsa take kamar xata yi kuka, ya langwabar da kai yace "Wasa fa nake" tace "Yeah na sani, bude min kofa in wuce" yace "Nooo baby i was only joking" bata ankara ba sai ji tayi ya wani sureta ta runtse ido tace "Doctor....." Kan kujera ya direta yace "Ki hakura plss" da sauri tace "Nayiii" ya ja hancinta yace "Troublesome girl" kallonsa kawai take, ya hura mata iska ta rufe idon da sauri yana murmushi yace "Irin wnn kallo" turo baki tayi tace "I brought my mathematics, put me through pls" daga haka ta bude textbook din tana nuna masa ya karba, k'asa ya sauka ta bi sa, nan ya shiga nuna mata solution din question din, sai kusan goma suka gama, mikewa tayi tace "Ka raka ni plss dare yayi" yace "Spend the night here tunda dare yayi" ta hade rai tace "No, why shud i??" kamo hannunta yayi ya tsare ta da ido yace "Cinye ki xan yi idan kin kwana?" Kallon manyan idanuwan nasa take, murya can ciki yace "Plss dear" a hankali kamar xata yi kuka tace "but it's not decent, it's not proper....." Da sauri yace "Naga dare yayi ne fa..." Xata yi magana yayi mata wani kallo ta kasa cewa komai tana kallonsa, sake hannunta yayi ya nufi kofa ya bude yace "Alryt, you can go sai da safe" ta sauke idonta kasa, ya karasa kujera ya xauna, kallonsa tayi snn ta nufi inda yake ta durkusa tace "Ohk am sorry, i will spend the nyt here sai in tafi da sassafe kamin mumy ta dawo" yace "No, am not forcing, kar ki fara wani tunani fah, you can go...." Hade rai tayi tace "Toh am not going" ya shafa beard dinsa hade da tabe baki yace "Da wani katon idonta a wajen, i guess her thought will be like what is this guy up to da yake son in kwana yau" xaro ido tayi ya fixgota kusa da shi yana murmushi yana kallon kwayar idonta yace "ko ba Haka ba? Babu abinda xan maki har sai ran da Allah ya mallaka min ke a matsayin matata" buda ido tayi tana kallonsa tace "Matar ka kuma" ya kai fuskarsa dab da nata yace "Ko baxa ki iya aurena ba" xaro ido tayi da mamaki xata yi magana ya rufe bakinta yana murmushi yace "Yesss" daga haka ya mike ya fita ya rufe gate snn ya dawo ciki ya rufe kofa ta bi sa da kallo har ya xauna yace "Za kiyi wanka?" Ta girgixa kai yace "Alryt shiga ki gyara inda xa ki kwana ni parlor xan kwanta before then bari inyi wanka" binsa tayi da ido har ya shiga dakin sai kuma ta bi bayansa, taga har ya shige bathroom, kallon gadon tayi taga it's tidy except from the bedsheet wanda hakan ya nuna alaman yayi bacci a kai, ta karasa ta shiga gyarawa tana gamawa ta dau wayarsa dake gaban mirror ta fara game, har ya fito bata sani ba, sai jin kamshi me dadi hade da ruwa da ya diga a jikinta, da sauri ta dago suka ci karo, ta mike tace "Ohhh sorry" yace "Uhm ohk" sauke idonta tayi ta mayar ga wayar ya nufi gaban mirror, har ya gama shiryawa bata kalli inda yake ba, sai bayan da ya gama ya dawo ya xauna kusa da ita yace "Kina da paper gobe?" Ta girgixa kai tace "Sae Tuesday" kallon game din da take yayi tayi, can ta mika masa wayar tace "Za kayi amfani da shi?" Ya girgixa kai yace "No, i just want you to tell me a story, may be a bible story, i like them, No! Ko kuma mu ci gaba da wanda nake baki ranan" ta kallesa tace "Toh barin in fara baka sae ka ci mim gaba, wani iri kake so?" yace "ko wanne" ta langwabar da kai tace "Ohk let me tell you the story of Joseph you will like it" yace "Tohm" hawa gadon yayi ya nuna mata kusa da shi ta turo baki tace "Nan ma yayi" yayi murmushi yace "Ohk" shiru tayi sai kuma a hankali ta hau ta dawo kusa da shi, nan ta fara basa story din Joseph according to the new testament of their Holy Bible, jin shirun yayi yawa ta dago tana kallonsa taga idonsa lumshe, murya can kasa tace "Doctor..." taji shiru, tsura ma long lashes dinsa ido tayi snn ta sauke idonta kan cute lips dinsa, bacci yake hankalinsa kwance, murmushi tayi ta gyara masa kansa a hankali snn ta koma can karshen gadon ta kwanta ta juya masa baya, nan da nan ita ma bacci ya dauke ta, can cikin dare ya farka ya mike xaune da sauri ta dalilin hasken dakin don wuta a kunne yake har lkcn kuma dama shi bai saba kwana da wuta ba, ya juya ya kalleta yaga ta dukunkune gu daya tana bacci don sanyi ne sosai a dakin ta dalilin ac da ya kure, sauka yyi daga kan gadon ya shiga toilet ya fito snn ya dauko duvet ya dawo kusa da ita ya lullubata da shi ya durkusa kusa da ita yana kallon kyakkyawan fuskarta, lumshe ido yayi ya kai lips dinsa goshinta snn ya mike ya kashe wutan dakin ya koma inda yake ya kwanta. Da asuba a gefensa ya ganta, ya mike zaune bayan ya karanto addu'ar tashi a bacci, ya kusa minti biyar xaune kafin ya mike ya shiga bayi don yin alwala ya wuce masallaci. Ko da ya dawo daga masallaci bata tashi ba, ya cire bargon jikinta ya ja hancinta, mikewa xaune tayi ya wara mata ido yace "Come and start going kar mumy ta dawo" kallon agogo tayi da sauri ta xaro ido, sai kuma ta mike tsaye ta cire kimonon jikinta ya rage daga ita sai half nighty ta shiga bayi, wanke fuskarta tayi ta wanke bakinta da freshener snn ta fito, xaune ta gansa kan darduma da Al-quran a gabansa, dago kai yayi yana kallonta ta karaso ta duka d'an nesa da shi tace "Good morning" ya wara mata manyan idonsa yace "Good morning Baby, kin tashi lafiya" xaro ido tayi tace "Ni kuma?" mikewa tayi tana murmushi ta dau kimononta ta saka ta tattara books dinta tace "Xan tafi" yace "Toh bari in raka ki" da sauri tace "No thank you" daga haka ta d'aga masa hannu ta nufi kofa ya bi ta da ido har ta fita. Karfe hudu da kusan rabi Abuturrab ya dawo daga gun aiki, wanka yayi ya shirya cikin kananun kaya ya fito, kallo daya yayi ma abincinsa da ke ajiye parlor ya fita, main house ya nufa, ya tadda Mami xaune parlor mai aiki na yi mata gyaran gashi, ya xauna ya gaisheta ta amsa tace "Har ka dawo?" Ya jinginar da kansa jikin kujera yace "Na dawo Mami" tace "Toh ka ci abinci?" Girgixa mata kai yayi yace "Ban ci ba tukun" tace "an kai maka can ai" yace "Na gani!" Mikewa yayi ya wuce sama. Yana dakinsu Ramla ta shigo, ta karaso tana kallonsa ganin ba yanda ta saba ganinsa ba ta xauna gefensa tace "What's wrong with you Aliyu?" Kallonta yayi yace "Nothing Mami" tace "ko dai kana son dawowa nan ne?" Murmushi yayi yace "Not at all" ta tabe baki tace "Toh kai ka sani" Shafa kansa yayi yace "Mami a kan maganan da Yakumbo ta min ranan" shiru tayi tana kallonsa sai kuma tace "Toh ya aka yi" ya langwabar da kai yace "I don't know what to do mum" ta tabe baki tace "yanxu duk yan matan da kake bani mu gaisa a waya ina suke?" Dariya yayi yace "Ohhh Mami na fa ce maki they are my frnds!" Tace "Toh, kana son in maka zabi?" Kallonta yayi da sauri yace "No Mami ni fa ina da warce nake so" tace "Toh kuma shine xa ka taho nan kana damuna" ya marairaice yace "Shawara fa na xo nema Mami" Mami tace "Toh ina jin ka, yar ina ce?" Shiru yayi yana kallonta, tace "Kayi shiru!" Xai yi magana aka bude kofar dakin, Khaleesat da Ilham suka shigo da alamar daga boko suke, mikewa yayi yace "Xa muyi magana anjima Mami" bin sa da kallo tayi, Su ilham suka gaishesa a tare, bai ko kallesu ba ya fice, khaleesat ta tabe baki, Ilham tace "Mami kin ga ya daina amsa gaisuwar mu koh?" Mami tace "ku kuka san me ya hada ku da shi ba ruwana" juyawa khaleesat tayi ta fice ilham ta bi bayanta, suna shiga dakinsu Ilham tace "You know what leesat, mu je mu basa hakuri, he's ignoring us" kamar xata yi kuka ta kare maganar, khaleesat na kokarin cire kayan jikinta tace "Am going no where" Ilham tace "Why?" Wani kallo Khaleesat tayi mata tace "Don ma ba mu gaya ma Mami abinda muka gani ba" ilham tayi shiru tana kallonta. Abuturrab na xaune parlornsa yana kallo a laptop misalin shidda da yan mintuna yaji an bude gate, kallon kofa yayi da sauri, aka turo kofar a hankali ta shigo rike da basket dauke da abinci, sosai abayar jikinta yayi mata kyau, ta karaso parlon ba tare da ta bari sun hada ido ba ganin kallon da yake mata, d'an nesa da shi ta xauna tace "Good evening, i brought you food" wara ido yayi ya mike tana ganin haka ita ma ta mike da sauri tayi hanyar kofa, suka ji an kwankwasa kofar, still tayi tana kallon kofar, kawai gani yayi ta juya da sauri tayi hanyar bedroom, aka bude kofar, ilham ce ta shigo ta tsaya daga bakin kofa tana kallonsa kamar xata yi kuka tace "Ya Abu ni dai kayi hakuri....." Ya hade rai yace "Me ya faru da xan yi hakuri, fitan min a parlor" tace "Plsss am sorry sweet bro" xai yi magana ta karaso ta rungumesa tace "Yayana plss mana" shiru yayi bai ce komai ba, a hankali tace "Kaji" janyeta yyi jikinsa yace "Toh tafi daki ki ba ta hakuri right away" dago kai tayi ta kallesa, sai kuma ta kalli hanyar dakin snn ta tafi, tsaye ta ganta ta juya baya, da sauri ta juyo tana kallon Ilham, Ilham ta karasa kusa da ita tana turo baki tace "Kiyi hakuri, we are sorry for everything...." Shiru samantha tayi tana kallonta ko kiftawa bbu. *Haske writers asso*📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 19.....😍😍 Ilham ta juya ta fita xuwa parlor tana kallonsa tace "Ya Abuu na bata hakurin" yace "And promise you two will be frnds daga yanxu" ta langwabar da kai tace "that's a promise, we re frnds now" yace "Good!" Murmushi tayi tace "Bye xamu tafi islamiyya" daga haka ta juya ta fita, bedroom ya shiga ya sameta tsaye har lkcn, ya rungume hannayensa yana kallonta, sunkuyar da kai tayi xata fita ya jawo ta yace "Ina xa ki?" Ba tare da ta kallesa ba tace "Gida xan koma" kallonta yayi daga sama har kasa murya can ciki yace "I love ur dressing...." Kwace kanta tayi ta fita da sauri, ya bi ta da ido, sai da ya ji fitar ta sannan ya fito parlor ya xauna ya bude abincin da ta kawo masa, pounded yam ya gani da vegetable soup yayi murmushi ya rufe warmer din hade da lumshe ido. Bayan kwana biyu yana xaune gaban gate da yamma yana danna waya sai dai da biyu yake xaune gun don for the past 3 dayz bai ga Samantha ba, duk ya koma kamar mara lafiya sai dai har kusan magrib bbu alamar ta. Washegari friday yana xaune office yana danne dannen laptop, tun xuwan sa hospital bbu patient din da yayi attending ma, aka kwankwasa kofarsa ya bada izinin shigowa wata nurse ta shigo rike da file ta ajiye gabansa tace "Xaka duba patient sir" yace "Ohk" ba tare da ya dago ba, ta juya ta fita ba a dau lkci ba ta dawo tare da wani mutumi da baxai wuce shekaru arba'in da bakwai ba, fari ne dogo da ganinsa ka ga bafulatani sbda kyansa, kallon mutumin Abuturrab yake har ya karaso ya xauna, suka gaisa Abuturrab ya bude file dinsa ya duba sunansa ya ga Mr David, kallonsa ya kuma yi sannan ya fara masa tambayoyi yana rubuce rubuce a white sheet dake cikin file din, sai da ya gama yayi gwaje gwajensa sannan ya koma ya zauna yace "Sir kana bukatan hutu sosai sbda bp dinka...." Mutumin yace "Toh xa a kiyaye, magunguna kawai nake so doctor" Abuturrab yayi murmushi yace "Da dai ka bari a hada da allura...." mutumin yace "No xan yi tafiya ne in 3 dayz" Abuturrab yace "Why not ka bari sai ka gama karban medication dinka, u need rest sir" mutumin ya girgixa kai yace "Tafiyar is urgent" Abutuurab yace "Ohk ba Abuja kake ba?" Mutumin yace "Nan nake" Abuturrab na son tambayarsa anguwar da yake amma ya rasa ta ya, bell ya danna don alerting din nurse, Mutumin yace "yanxun ma don family doc dina bai garin ne shi yasa na taho asibiti" Abuturrab ya dake yace "Ohk, wani anguwar kake?" Mutumin ya kallesa ya fada masa, Abuturrab yace "Ohk, nima anguwar nake kuwa, if you don't mind idan na dawo ltr sai in karasa in baka injections din, xan ma iya dinga xuwa can gidan ina baka medication din har ya kare, but that is if you are okay by that" mutumin yace "Alryt, am greatful Dr, ga digit dina sai ka kira ni" karban complimentary card dinsa yayi, ya kalli nurse din dake tsaye ya mika mata file din yace "Drugs only" daga haka Mr David ya mike yayi masa godiya ya fita, Abuturrab ya lumshe ido hade da murmushi murya can kasa yace "Samha's father!" Abuturrab na dawowa daga mosque da magrib ya dau mota ya tafi pharmacy ya siya drugs da allurai, ya jima xaune a motarsa bayan yayi parking a kofar gidansu Samantha, can ya dau wayarsa ya ciro complimentary card din da Mr David ya basa ya kwashe numbers din yayi dialing, sai da ya kusa katsewa ya dauka, mancewa Abuturrab yayi yace "Assalamu alaikum" daga daya bangaren Mr David yace "Yes, who's on the line?" Abuturrab ya ce "Ohh sorry, it's Doctor Aliyu... You remember?" Mr david yayi shiru, can yace "Ohh Doctor how you?" Abutturab yace "Am fine, am at ur premises, at the gate" Mr David yace "Ohk, you can come in...." Abuturrab yace "Alryt!" Daga haka ya katse wayar ya bude motar ya fito ya nufi gate ya bude ya shiga, gaisawa suka yi da mai gadi, mai gadin ya tambayesa wanda yake nema yace mai gidan ya kuma sanar da shi he's a doctor, har kofar da xai sada shi da main parlor din gidan mai gadin ya kai sa, mai aikin gidan ce ta bude kofar, ta gaida Abuturrab ya amsa ya shiga parlon yace "Ki yi ma mai gidan magana, you tell him his doctor is around" sama ta nufa ta bar sa nn tsaye yana kare ma makeken parlon da ya tsaru da kayan alatu, ba a dau lkci ba ta dawo tace "Yace ka tafi dakinsa" yace "ohk" kitchen ta wuce shi kuma ya wuce sama da sauri ya juyo tunawa da yayi bai san bedroom din ba ya ga har ta shige kitchen, kamar me tsoron staircases din haka ya dinga taka su har ya isa sama ya tsaya yana bin corridor din rooms din da kallo, bude wani kofa aka yi samantha ta fito sanye da mini skirt fari sai vest hannunta rike da system, still tayi inda take tana kallonsa da mamaki kuma a tsorace, ya wara mata manyan idanuwansa yana murmushin sa mai kyau yace "Sweetheart!" Bude kofa aka yi Dad dinta ya fito, da sauri ta juya ta koma cikin daki, Abuturrab yace "Good evening sir" Murmushi dauke fuskarsa yace "Welcome Doctor, shigo" bin bayansa Abuturrab yayi suka shiga dakinsa, bbu 6ata lkci cikin minti sha biyar Abuturrab yayi abinda ya kawo sa, Mr David ya dauko dubu ashirin a take ya basa, yana shafa kai yace "No sir, sae na gama treatment din" Mr David yace "Alryt, na gode kwarai, a ina kake a nan anguwar?" Abuturrab yace "Just few houses away bbu nisa" hannu Mr David ya basa ya kuma yi masa godiya yace "Yaushe xa ka xo gobe don xan fita" Abuturrab yace "May be da yamma idan na dawo daga gun aiki" Mr David yace "Alryt, xaka taho ma Daughter na da Malaria drugs" Abuturrab yace "How old is she? Tayi test ne?" Girgixa kai yayi yace "No, ba ayi test ba, but i guess it's malaria, she's 19...." Abuturrab yace "Ohk, tana kusa ne?" Mr David yace "Yes, bari in kirata" daga haka ya fita, bayan yan mintuna ya dawo dakin, bai jima da shigowa ba Samantha ta shigo, wannan karan sanye take da doguwar riga, bata bari sun hada ido da Abuturrab dake ta kallonta ba, Mr David yace "Gata" Abuturrab yace "Sannu...." Satan kallonsa tayi tace "Ina yini" yace "Lafiya, how are you feeling, i mean ina ke maki ciwo?" Ba tare da ta kallesa ba still tana fidgeting fingers dinta tace "Ciwon kai!" Yace "Just ciwon kai?" Shiru tayi sai kuma tace "Ina amai kuma" yace "Amma kina cin abinci?" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa suka yi ido hudu, kasa daina kallonta yayi ganin yanda ta rame, ta sunkuyar da kanta da sauri, shima ya dauke kai yace "Me yasa ba ku je asibiti ba sir?" Mr David yace "Ta ki yarda babu yanda uwarta bata yi su je ba ta ki" Abuturrab yace "Ohk xan kawo mata magani gobe, but still ya kamata ayi test" Mr David yace "Alryt thank you doctor ko gobe sai ayi test din...." Sallama Abuturrab yayi masa ya ya kuma kallonta ita ma kallonsa take ya nufi kofa ya fita, Blessing na parlor har ya kai kofar fita ya juyo ya ciro biro aljihinsa da takarda yayi rubutu ya ciro kudi ya hada snn ya karasa kusa da ita yace "Hello, plss ki ba Samantha, plss" kallonsa tayi ta kalli kudin sannan ta karba tace "Toh xan bata" fita yayi yana tunanin anya hakan da yayi ya kamata don bai ma san halin yarinyar ba, yana isa gida ya xauna parlor ya jinginar da kai jikin kujera ya lumshe ido. Samantha na xaune daki tayi shiru tana tunanin yanda Abbanta yasan Abuturrab blessing ta shigo tace "Sister Rebecca, the doctor gave me this to give you, ya hada har da kudi ya ban" da sauri Samantha ta karba tace "Ohk ohk, don't say anything about it blessing" kudin ta mika mata Samantha tace "A'a tafi da shi" tana fita Samantha ta bude takardar ta karanta content din "Plss plss ki xo gida yanxu am waiting, don't ignore dear" *Haske writers asso*📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 20..... Ta koma ta kwanta a hankali, can kuma ta mike xaune tayi tagumi, to ko taje ne, tunanin da take kenan, kawai ta mike ta kashe wutan dakinta ta bude kofa a hankali ta fita, blessing na parlor ta karasa kusa da ita tace "Blessing idan Abba ya kirani kice masa nayi bacci" Blessing tace "Toh" kamar munafuka ta fita gidan ta dau hanyar gidansu Abuturrab, a hankali ta tura gate ta shiga ta karasa balcony ta bude kofar parlor ta shiga, mikewa yayi yana kallonta ya nufeta yayi murmushi yace "Thanks dear!" Ta langwabar da kai tace "What's the call about?" Hannu ya sa a goshinta yaji xafi yace "Tun yaushe ne baki da lafiya?" A hankali tace "Since" ya kamo hannunta da damuwa yace "And you didn't tell me, wani maganin kike sha?" Janye hannunta tayi tace "How did you know my dad?" Murmushi yayi yace "Kin raina kitaba ta ne?" Bata ce komai ba, ya kama hannunta ya xaunar da ita kan kujera yace am coming, bin sa tayi da kallo ya shiga daki, can ya fito rike da stethoscope da thermometer, ya dawo kusa da ita ya xauna yana kallon kirjinta murya can kasa yace "how will i get to ur chest?" Ta masa wani kallo tace "What?" Murmushi yayi yace "Yeah, i want to use my stethoscope on u!" Tace "Toh bana so!" Wani kallo ya mata ya jawo ta kusa da shi ta xaro ido xata yi magana taji hannunsa a bayanta, a hankali ya xuge xip din ya sauke doguwar rigar kasa ya rage farin vest din jikinta, wani kallo take masa xata yi magana ya daura fingers dinsa guda biyu a lips dinta yana kallon cikin oily eyes dinta, daukar stethoscope din yayi ya makala a kunne, snn ya daga vest din a hankali ya manna daga kasan kirjinta, lumshe ido tayi, shi ko sai kallonta yake, can ya lumshe nasa idon ya cire instrument din ya ajiye ya sauke vest din, ya mayar mata da rigarta ya ja zip ya mike, sai a snn ta bude ido taga daki ya wuce, ba a dau lkci ba ya dawo da magunguna har da allura, tana ganin haka tace "Baxan karba allura ba" bai tanka taba ya xauna ya gama hada alluran snn yace "Kin shirya" bai jira tace komai ba ya mike yana kallonta yace "Am waiting" kamar xata yi kuka tace "Ni bana so nace" hade rai yayi ya dago ta, bata ankara ba sai ji tayi yana kkrin daga mata riga tace "Noooo" ya wani daure fuska yace "What?" Kamar xata yi kuka tace "Doctor there's nothing inside, just..." Dariya ta basa ya dake yace "Then???" Bata ce komai ba ta marairaice tana kallonsa, yace "Ohk Alryt!" Kama hannunta yayi ya isa gun switch din wutan ya kashe, duhu ya gauraye parlon, ya daga rigar gaba daya tace "Doctorrrr..." Dafa bango tayi ta runtse ido jikinta na rawa, har ta ji ya xare alluran, bata ankara ba taji ya rungumeta ta baya ya daura kansa a shoulder dinta murya can kasa "Get well soon wife" bude ido tayi da sauri, ya juyo da ita yana kallonta cikin duhun yace "Ki bar wahalar da ni Samha, stop pretending you don't know where i am heading, i know you know....." Rungumeta yayi cikin sanyin murya yace "I love you!" Ita dai bata iya tace komai ba, ya matse ta jikinsa yace "Kice abu mana dear, talk plsss" kamar mara lafiya yayi maganan, ta lumshe ido a hankali tana jin yanda xuciyarsa ke bugawa, harde hannunta yayi da na shi murya can kasa yace "Talk plss, say something Samha" ta rasa abinda xata ce, shafa bayanta ya fara yi a hankali ya kai bakinsa wuyanta, ta bude ido da sauri jin saukan numfashinsa a jikinta, lkci daya jikinta ya dau rawa da kyar tace "Doctor stop pls...." Cikin kasalalliyar murya yace "Talk! second love" Ta kuma runtse ido jin ya ki dauke lips dinsa a wuyanta, murya can kasa tace "I... I... I... Love you tooo" wara ido yayi ya saketa yace "Da gaske baby??" Ja baya ta dinga yi kawai sai gani yyi ta juya a guje ta nufi kofa ta bude ta fice. Washegari asabar da yamma Abuturrab ya iso gidan Mr David da da magungunan da xai ba Samantha jiya ta gudu, Mumy ya tarar xaune parlor tare da Mr David din bayan an masa izinin shigowa ya gaisheta ta dinga masa wani kallon mamaki, Mr David ya mike yace "Likitan da nake fadi maki kenan" daga haka yace ma Abuturrab ya taho sama, Abuturab ya bi bayansa suka wuce saman, yau ma bbu wani 6ata lkci ya gama basa medication din, ya tambayi samantha, Mr David yace ta tafi church, shiru Abuturrab yyi sai kuma yace "But da ta hakura har ta samu sauki" mika masa magungunanta yayi, yayi masa sallama ya fita, Sai da ya isa kofar fita sannan ya juya ya kalli Mahaifiyar Samantha ya ga kallonsa take yi, yace "Sae da safe Ma!" Wani kallo tayi masa ta mike fuu ta wuce sama, yayi murmushi ya fita, a bakin gate ya hadu da samantha, tana ganinsa ta koma baya da sauri, motarsa ya nufa ya tsaya ya rungume hannayensa yana kallonta har xata shiga gate sai kuma ta tsaya ta d'an saci kallonsa taga idonsa na kanta, kamar mai counting step ta nufi inda yake ta tsaya nesa da shi, tace "Good evening!" Yace "Da wucewa xa kiyi?" Kallonsa tayi suka hada ido tayi murmushi ta girgixa kai, ya lumshe ido yace "Come here" tace "Ba gani ba?" Ya harareta ya nuna mata gabansa, kamar xata yi kuka tace "Kaga daga church fa nake, am tired! Am feeling dizzy" Yace "To tafi...." Shiru tayi tana kallonsa, can ta karaso gabansa a hankali tace "Gani" dago kanta yayi yana kallon kwayar idonta yace "Me yasa kika fita baki da lafiya?" Ta sauke idonta tace "I went to church, Mumy tace in je" Wani kallo yayi mata yace "To daga yau kar ki sake xuwa har sai kin samu lafiya...." Ta xaro ido, ya gyada kai yace "yes I mean it...." Tace "to ae addu'a ake min a can ma" ya tabe baki yace "Good sai kiyi ta xuwa...." Kallonsa ta tsaya yi, ya juya ya bude motarsa ya shiga ya tada, ta lumshe ido ta bude tace "Ohk ohk, baxan je ba kuma" hararanta yayi, tayi kamar xata yi kuka tace "I mean it baxan je ba...." Yace "Better! Taho ki ji" karasawa tayi kusa da glass din motar tace "Mene?" Yace "Matso mana" matsowa tayi, dai dai kunnenta yace "Drugs dinki da prescription na gun Abba, you make sure you take all before going to bed, since you ran away yesterday....." Bata jira ya karasa ba ta juya da sauri don gaba daya ta mance da incident din jiya, ya rikota da sauri ya jawota yayi planting mata kiss a cute lips dinta, ta kwace kanta da gudu ta shiga gida. Ranan litinin Samantha ta kare exams dinta na Waec, karfe uku driver ya je dauko ta a sch, kamar ko da yaushe a bakin layi ya ajiyeta ta karasa wai xai je kasuwa Mumy ta aikesa, tana isa dai dai gidansu Abuturrab ta ga motarsa a waje, ta tsaya tana kallon gate din ko me ta tuna kuma ta fasa shiga xata wuce aka bude gate, sai ga shi ya fito, wara ido yayi ganinta yace "Ina kuma xa ki?" Tace "Wucewa nake yi ai" yace "Uhm, i see yaushe xa ku gama waec din?" Tace "Mun gama" yace "Waow da gaske baby, but shine baki fada min ba?" Ta langwabar da kai tace "Gashi na gaya ma!" Yace "Alryt... Plss ki xo anjima da yamma i have a surprise for you, yanxu xan tafi gun aiki ne i forgot my office key...." Tace "Baxa a bar ni in fito ba...." Xai yi magana aka bude gate sai ga Mami ta fito, gaba daya ya mance tace xai ajiyeta a hanya, kallo daya Mami tayi ma Samantha tace "Aliyu da ban fito ba wucewar ka xaka yi knn?" Ya shafa kai yace "Ohh Mami wllh mancewa nayi...." Samantha da ko ba a gaya mata ba ta gane mum dinsa ce ganin kamar da suka yi da Hajiya Mariya ta risina tace "Ina kwana..." Mami ta kalleta murmushi dauke fuskarta tace "Lafiya lau yan mata ya makaranta" murmushi kawai samantha tayi kanta a kasa tace "Sai anjima...." Daga haka ta juya ta wuce, Mami ta bude bayan mota ta shiga Abuturrab ya shiga motar shi ma ya tada, sai da yayi reverse Mami tace "Ina ka samo wnn kuma?" Ta madubi ya kalleta yace "A anguwar take, she's.... A frnd!" Mami tace "Amma ba musulma bace?" Shiru yayi na kusan minti hudu, cikin sanyin murya yace "Me kika ga Mami?" Mami dake danna waya tace "Me na gani a ina?" Yace "Da kika ce ba musulma bace" Mami da har ta mance xancen da suke tace "Ae musulinci ba boyayyen addini bne, duk inda kaga musulmi xaka gane....." Yace "But Mami uniform ne fa jikinta with Beret!" Tace "So? 'Ya mace musulma dai da ta taso gidan tarbiya baxata bar gida xuwa makaranta ba hijab ba, ko da kuwa makarantar ba a saka hijab xata sa d'an karami idan ta isa gate ta cire..." Abuturrab da idonsa ke kan titi murya can kasa yace "But mami ae lullubi ba shine abinda xai sa ka gane mutum me addini ba, a xuci....." Tunda ya fara Mami ke masa wani kallo bata bari ya kai aya ba a tsawace tace "Meye hadin ka da yarinyar nan Aliyu, who is she?" Shiru yayi har sai da tace "Baka ji na ne?" A hankali yace "She's just a frnd Mami...." Tsaki tayi ta ci gaba da danna wayarta, bai sake cewa komai ba har ya isa inda xai ajiyeta, yayi parking ya juya yana kallonta yace "Mun kawo Mami" bude motar tayi ta fita tana kallonsa tace "Yaushe xaka koma gida?" Yace "Zan bar clinic karfe hudu" tace "Ohk...." Yace "Xan biyo in dauke ki ne?" Tace "No, kafin lkcn ni na koma gida..." Daga haka tace "Allah ya tsare" sannan ta shiga gidan, ya kusa minti uku kafin ya ja motar jiki a sanyaye ya bar wajen. Karfe biyar da wani abu yana xaune kofar gida yana danna waya blessing ta xo wucewa, mikewa yayi da sauri ganinta yace "Hello!" Ta juya tana kallonsa sannan tace "Ina yini?" Yace "lafiya lau, plss wait in baki sako ki ba Samantha!" Da sauri ya shiga gida ba a dau lkci ba ya fito rike da takarda a linke ya mika mata tare da dubu daya yace "Ki bata pls" karba tayi tace "xan bata, nagode" daga haka ta wuce, ya sauke ajiyar xuciya ya koma ya xauna. Samantha ta fito daga wanka bayan magrib blessing ta bude kofar dakinta ta karasa da sauri tace "Sister Rebecca wannan Doctor din yace in baki takardan nan..." Da sauri Samantha ta karba Blessing ta juya ta fice kafin Mumy ta fara nemanta, xaunawa tayi gaban mirror tana goge jikinta tana gamawa ta dauko lotion ta fara shafawa sannan ta dau turarruka fiye da kala biyar ta feshe jikinta da su, sai da ta gama ta dau takardan ta bude, rubutu ta gani kamar haka "ki taho don Allah am waiting for you love...." Ajiye takardar tayi hade da tabe baki ta mike ta dauko kayan baccinta ta saka snn ta tusa gashinta a net, ta kusa minti talatin xaune, can ta mike a hankali ta bude closet dinta ta dauko daya daga hijabs din da take sawa lkcn sanyi ta saka shi har kasa, ta kashe wutan dakinta ta fita, tana waige waige kamar munafuka har ta fita daga gidan. Ta jima tsaye bakin gate din gidan kafin ta tura a hankali ta shiga ta rufe, bbu kowa parlon ta tsaya bakin kofa tana kare ma ko ina kallo, fitowa yayi daga bedroom, yayi murmushi yana kallonta ya karaso yace "Woaw she came!" Rufe kofar yayi yasa key yace "Welcm love" ta hade rae tace "me yasa kace in xo?" Yace "I just want to see you" turo baki tayi tace "Bude min kofa in wuce...." Wara ido yayi yace "Noo, not until you repeat what you said yesterday...." Juyawa tayi da sauri tace "Noo, plss ka bar ni in wuce..." Murmushi yayi yace "Then ashe xa ki kwana a nan" kamar xata yi kuka tace "Plsss..." Ya daga kafada yace "Ohk let see" daga haka ya tafi three seater yayi kwanciyarsa, ji tayi kamar ta fashe da kuka, wayarsa ya dauka ya jona earpiece ya makala a kunne hade da lumshe ido, ta kusa minti talatin tsaye parlon ganin ya ki cewa komai ta juyo a hankali ta ga har lkcin idonsa a lumshe suke, can ta karasa kusa da shi ta duka tana kallonsa sae ta ga kamar bacci yake, kasa dauke idonta a fuskarsa tayi, can ta cire earpiece daya a hankali ta kai kunne taji karatun Qur'ani yake ji, mayar masa tayi, ta matsa kusa da shi har lkci tana kallonsa, a hankali tace "I... I said i... Love you!" Kallon fingers dinsa tayi ta kai hannunta tana kallon Ring din azurfan dake hannunsa har biyu, lumshe ido tayi ta daura lips dinta a hankali, rike hannunta yayi ta sake sa da sauri duk ta daburce xata mike ya ki saketa ya mike xaune. *Haske writers asso*📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 21..... Kin bari su hada ido tayi tana girgixa kai tace "Doctor plss ka sake ni..." Yace "Noo..." Kwankwasa kofa aka yi suka kalli kofar a tare, ta xaro ido tace "Wayyo ka sake ni..." Saketa yyi ya mike yana kallon kofar, ta tashi da sauri tayi hanyar bedroom, karasawa gun kofar yayi yace "Waye?" Muryar Ramla ya ji tace "Ni ce!" Yace "What?" Tace "Abba yana kiran ka wai..." Yace "Alryt ga ni nan xuwa" tace "Toh baxa ka bude ba yaya?" Yace "Yess" tabe baki tayi ta juya ta wuce, juyawa yayi ya shiga bedroom din ya ganta tsaye bakin kofa, tana ganinsa ta juya, ya rungume hannayensa yace "Ashe kina sa Hijab?" Shiru tayi bata ce komai ba, yace "Ina wayar da na baki?" A hankali tace "Yana gida!" Ya juyo da ita yana kallon fuskarta yace "ki ajiye shi kusa da ke yau, i will cal you" ta sunkuyar da kanta tace "Toh" yayi murmushi yace "Mu je in raka ki" hanya ya bata ta fita sannan ya fita shi ma, har kusa da gidansu ya rakata yana kallonta yace "Kar kiyi bacci fa, i will call you..." Daga haka ya juya ya wuce ta bi sa da kallo, snn ta nufi gate kamar mara laka ta shiga. Abuturrab na isa gida ya wuce parlor din Abbansa, Abba dake waya tun shigowarsa ya ajiye bayan ya gama yace "Aliyu!" Abuturrab yace "Na'am..." "Kadai san in ka raina ni to yakumbo ta wuce raini a gun ka koh?" Cewar Abba kenan yana kallonsa, Abuturrab ya sunkuyar da kai ya kasa cewa komai, Abba yace "Tashi ka je...." Ba musu ya mike murya can kasa yace "Kayi hakuri Abba dama..." Kofa Abba ya nuna masa, hakan yasa ya fita kawai, sha biyu saura ya gama abinda xai yi ya rufe laptop snn ya dau wayarsa yayi dialing layinsa dake wayar da ya ba Samantha, tana kwance hannunta rike da hymn book tana dubawa kiran ya shigo wayar dake gefenta, langwabar da kai tayi ta dauka ta yi picking ta kai kunne, daga daya bangaren yace "Hope baki yi hacci ba?" Tace "Yanxu xan yi..." Yace "Tafi ki wanke idon..." Murmushi tayi ta make kafada kamar yana ganinta, yace "Ina son in maki wani tambaya samha..." Tace "Samantha not samha..." Yace "Noo samha not Samantha.." Tace "Uhm to ina jin ka..." Shirun kusan second ashirin yayi kafin yace "Za ki iya aurena?" Kasa cewa komai tayi sbda mamaki da ya cika ta, yace "I know you re there!" A hankali tace "Aure kuma?" Yace "Yeah.." Ta girgixa kai tace "But ae bbu aure tsakaninmu da kai, our religion differs, am a Christian, you re a muslim..." Yace "Akwai aure tsakaninmu...." Da mamaki tace "How?" Ya shafa kai yace "Sai kiyi addinin ki in yi nawa!" Wani shirun ta kuma yi words dinsa na mata yawo a kai, murya can ciki yace "Samha!" Kasa amsawa tayi, cikin sanyin murya yace "Baki so na kenan..." Jikinta yayi sanyi still ta rasa abun cewa, kiranta ya kuma yi kamar xata yi kuka tace "Ni ban san me xan ce ba..." Yace "Ki ce za ki aure ni" tace "you know that's very impossible, taya hakan xai yiwu bayan addininmu daban daban...." Lumshe ido yayi yace "Nace maki kowa addininsa xai yi, i see nothing wrong with that...." Rasa ma wani tunani xata yi a lkcn tayi, xata iya auren Abuturrab kuwa? Did she even love him? She know she so care about him.. Tunanin hakan sai da yasa gabanta faduwa sosai, to in ta yarda xata aure sa Mumy da Abba fa? Ya relative dinsu xa su dau xancen... Muryarsa taji yace "Samha!" Hawaye ne ya cika idonta ta kasa amsawa, da dadewa tasan she had alwayz like him, amma bata taba tunanin har xae shigo da xancen aure tsakaninsu ba, a hankali taji yace "Shikenan sai da safe" lkci daya hawayen idonta ya xubo cikin rawar murya tace "Doctor kasan baxai yiwu ba, My parent... My relatives, my...." Kuka ta fara masa, duk ya rikice yace "Kuka kuma... Pls stop it now" kasa daina kukan tayi, yace "OMG don nace xan aure ki shi yasa ki kuka, ok am sorry baxan sake ba..." Daga haka ya katse wayar, ya jefar gefensa ya kashe wuta yayi kwanciyarsa, hade kai tayi da gwiwa ta fara kuka, daga karshe ta gaji ta kwanta, kasa bacci tayi daren ranan, maganganun Abuturrab kadai ke mata yawo a ka, sae kusan karfe uku ta samu bacci ya dauketa, Mumy ce ta tasheta karfe takwas da minti sha biyar, ta mike xaune, Mumy tace "Baki tashi kinyi morning devotion din ki ba wnn wani irin bacci kika yi" Kallon idonta Mumy tayi tace "Me ya samu idon ki, kuka kika yi ne?" Samantha ta girgixa kai cikin sanyin murya tace "kai na ke min ciwo..." Mumy tace "Kai kuma? Toh tashi ki shirya sai kiyi breakfast ki sha magani," daga haka ta fita, da kyar Samantha ta mike tsaye don ji tayi gaba daya kanta ya mata nauyi, bathroom ta shiga ta wanke baki tayi wanka sannan ta fito, tana goge jiki Abuturrab ya fado mata wanda hakan sai da yasa gabanta ya fadi sosai, hawaye ya cika idonta, jiki a mace ta karasa shiryawa, Blessing ta shigo da tray dake dauke da breakfast ta ajiye mata ta gaisheta snn ta fita, da kyar ta iya shan tea xata kwanta sai ga Mumy ta shigo da magunguna ta bata ta sha, mumy tace "Thank God sai da ku ka gama jarabawa ciwon kan ya same ki, ki kwanta xuwa anjima mu ga" daga haka ta fita, Samantha ta kwanta hade da lumshe ido, ta kasa daina tunanin Abuturrab ta kuma rasa dalili, a da tasan yana yawan fado mata barin idan suka dade basu hadu ba, amma tun daga jiya da daddare xuwa yau sae ta ga ya fi na ko da yaushe, to fushi yayi ne yasa ya kashe wayarsa amma ai gaskiya take fada, runtse ido tayi ko bacci xae dauketa amma shiru, sae a lkcn tasan ashe fa ta damu da shi haka. Har washegari Abuturrab bai sake kiranta ba, ita dai tasan bbu wani ciwon kai but da Mumy ta tambayeta me ke damunta sai tace ciwon kai, tun da take abu bai taba tsaya mata a rai kamar yanda wannan ya tsaya mata ba, ta kasa dauke tunanin a ranta, Mumy ta kira Abba dake Lagos ta fadi masa bata da lafiya xa su je asibiti, Abba yace ba sai anje ba xae turo likita, Abuturrab na xaune office yana aikin gabansa, baka taba cewa abu na damunsa sai dai da xaka shiga xuciyarsa ka ga tulin damuwar dake tattare da gun sae ka tausaya masa, babban damuwarsa bai san yanda xae yi da Yakumbo ba don yasan shi ake ta jira, gashi ya kasa daina tunanin Samantha, yasan ba fault dinta bane that's just the fact but kawai ya shareta ya kuma dau ma kansa alkawarin ko ba yanxu ba sai ya aureta ko da kuwa threatening din kisa xa ayi masa, Tun a daren yake raya ma kansa to ko ya koma ga saudat, yana jin kuma xuciyarsa ta aminta da hakan coz he gat no option. Daren ranan ya shirya ya tafi gidansu Saudat, tun da yayi parking a kofar gidansu yake kallon motar dake parke gaba da nasa ganin kamar akwai mutane a ciki, ae ko sai ga shi an bude motar saudat ta fito, tabe baki yayi ya tada motarsa kawai yayi reverse ya bar gun, bai bar layin ba kiranta ya shigo wayarsa, ya ci gaba da tukinsa ba tare da ya sake kallon wayar ba. Washegari Wednesday yana xaune office ya hade kai da table Mujaheed ya shigo, har ya karasa gun table din Abuturrab bai dago ba, mujaheed ya bugi table din yace "Bacci kake a bakin aiki doctor?" Dagowa Abuturrab yayi yana kallonsa yace "Daga ina haka?" Mujaheed yace "Asibiti na xo bani da lafiya mana" murmushi Abuturrab yayi yace "Ohh i see" mujaheed yace "Ya na ganka haka kamar kana tare da damuwa" Abuturrab yayi yake yace "Damuwa kuma, am just tired ne, ya aiki?" Mujaheed yace "Alhmdllh" *Haske writers asso*📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 22...... Hira suka ta yi a asibitin har bayan la'asar suna fitowa daga masallaci ko wannensu ya dau hanyar gida, yau kam Abuturrab a main house dinsu ya sauka, Mami dake parlor ta bi sa da kallo bayan ya gaisheta har ya haura sama, wanka yayi ya fiddo jallabiyarsa a daki ya sa yayi kwanciyarsa. Ringing din wayarsa ne ya tashesa kusan magrib, dai dai shigowar mami dakin tace "Lafiyan ka Aliyu, baccin yamma ana xaune kalau?" Mikewa xaune yayi ya dau wayarsa yayi picking call din, daga daya bangaren aka ce "Hello!" Abuturrab yace "Good evening" "Evening, kana gida ne doctor" cewar mutumin kenan, sae a snn Abuturrab ya dau murya yace "Yeah ina gida sir, ya aiki?" Mr David yace "We Thank God, daughter na ne bata da lafiya, i want you to check on her if it's ohk by you and you re less busy pls" Abuturrab da hankalinsa ya tashi lkci daya yace "Ohk sir, i will do that right away!" Daga haka ya katse wayar ya kalli Mami dake tsaye har lkcn tana kallonsa yace "Mami na gaji da yawa ne yau" tace "ko abincin fa baka ci ba" mikewa yayi tsaye yace "Bari in dawo daga masallaci Mami" daga haka ya fita, ana idar da magrib ya tafi gidansu Samantha, bayan sun gaisa da mai gadin ya shiga, mai aiki ce ta bude masa kofa bayan ya danna bell, ya amsa gaisuwarta ya tambayeta inda Samantha take tace tana bedroom, ita ta raka sa har sama, ya bude kofar dakin suka yi ido hudu da mahaifiyarta dake xaune dakin alamar dai likita take jira, tana ganinsa ta hade rai sosai, ya sunkuyar da kansa ya karasa dakin ya gaisheta da ladabi, da hanci ta amsa masa ta mike ta fice, Abuturrab ya durkusa kusa da gadon yana kallonta ganin yanda lips dinta yayi ja, hannu ya daura forehead dinta ya ji dumi, a hankali yace "Samha..." Bude ido tayi da sauri ta mike xaune, ya kamo hannunta yace "Ina ke maki ciwo?" Hawaye ya cika idonta ta ki cewa komai, cire bargon jikinta yayi yace "Talk plss" ta sauke idonta kasa, ya tsura ma wuyarta dake dauke da farin cross ido, a hankali ya kai hannu kai xae tsinka ta rike hannun da sauri tace "Mumy ce ta sa min" bai kulata ba ya tsinka shi ya jefar gefe daya, ta sauke hannunta tana kallonsa, kallon kwayar idonta yake shi ma, hawayen da ke makale idonta ya gangaro ta daura kanta a shoulder dinsa cikin sanyin murya tace "Ni fa ban ce komai ba doctor, and you re angry, kayi hakuri pls..." Ya harde hannunsa da nata ya lumshe ido yace "Noo, kin fa ce baxa ki iya aurena ba" ta fashe da kuka tace "Nooo ni bnce haka ba fa..." Shiru yayi yana jin saukar hawayenta a shoulder dinsa, ya shafa kanta a hankali yace "But nace kiyi addinin ki inyi nawa fa, still kika ce it's impossible" girgixa kai tayi tace "Bayan kana rabani da duk wani abu na addini na shine xaka ce min haka, yanxu fa ka tsinka min rosary dina...." Buda ido yayi jin abinda tace, ya dago kanta yace "Ohh you gat me wrong samha..." Da sauri tace "Noo i am right" yace "You re sick kuma rosary din nan is a burden....." Hade rai tayi tace "A tunanin ka ba, kayan jikina bai xame min burden ba sai rosary" yace "Alryt am sorry baxan sake ba..." Bude kofa aka yi ya koma baya da sauri blessing ta shigo da gani kasan mumy ce tace ta taho, Ya kalleta yace "Taimaka mana da cup of tea pls.." Tace "Toh" snn ta fita, ya kamo hannunta yace "Toh yanxu ina ke maki ciwo" kanta ta nuna masa, yayi shiru yana kallonta, can yace ohk yanxun nan xae daina, lumshe ido yayi ya manna bakinsa kan goshinta, turasa ta fara yi tace "Doctorrrr" ya rike kanta gam ya sauko da ba lips din har kan hancinta sannan bakinta, yayi mata light French kiss, turasa tayi ta hade rai, ya wara mata ido ya koma baya yace "Alryt am sorry wife...." Blessing ce ta shigo da cup din tea ya karba ya mika ma Samantha, ta6awa tayi tace "Akwai zafi ai" ya ajiye sa kan bedside drawer yace "Toh bari inje in dawo yanxu" da ido ta bi sa har ya fita, gida ya koma ya dauko mata drugs ba a dau lkci ba ya dawo, har lkcn blessing na dakin, yayi mata kallo daya ya karasa gun Samantha ya dau tea din da ya ajiye ya kai baki yayi sip dinsa snn ya mika mata yace "Toh ya huce" hannu tasa ta karba, aka bude kofa Mumy ta shigo, mikewa yayi ya bude ledan maganin ya gwada mata yanda xata sha ya ajiye ya d'an saci kallon mumy ya ganta tsaye fuskar nan a murtuke, dukawa yayi kamar xae dauki abu murya can ciki yace "I will call you ltr..." Daga haka ya juya, bai bari sun hada ido da Mumy ba yayi mata sallama ya fita. Kamar jiya yau ma sha biyu da wani abu ya kirata, tana kwance ta dau wayar tayi picking ta kai kunne, daga daya bangaren yace "How you feeling now?" Tace "Da sauki..." Yace "Sai kice Alhmdllh..." Ta buda ido tace "Alhmdllh kuma?" Yace "Yess" tace "Tohm Alhmdllh" yayi murmushi yace "Good, a ina muka tsaya jiya a maganar mu?" Bata ce komai ba yace "Samha..." Cikin sanyin murya tace "Na'am" yace "Baki son maganan ne?" Girgixa kai tayi kamar yana ganinta tace "A'a fah" yace "Say something now" da kyar tace "Duk yanda kace doctor" murmushi yayi yace "Ohk we'll talk about that face to face...." Cikin sanyin murya tace "Toh" "Me xa ki bani for my birthday?" Wara ido tayi tace "Woaw, it's also my birthday month, wani date ne naka?" Yace "Da gaske kema month dinki ne?" Tace "Eh mana, my birthday is on 10th june...." Da mamaki yace "Are you for real?" Tace "Yes mana" yace "Woaww what a concurrent! It's same with mine" tace "heey doctor ba wani nan..." Yace "Am serious samha, i was also born on 10th june" tace "Wow so we re birthday mates?" Yace "Yeahh and we gonna celebrate it together.... No wonder shi yasa kike da kyau kema kamar ni... Haka kuma xa mu haifi yara duk june 10" Ta xaro ido tace "Uhm?" Yace "Yess am serious baby, today is 3rd, 7 dayz to our birthday!" Tun daga lkcn wayarsu ya xama constant don xaman gida kawai take, duk bayan awa biyu sai ya kirata, hakan kuma yasa bai damu da rashin ganinta ba tunda suna waya, a haka har ya rage kwana daya birthday din nasu, da daddare yana daki ya kirata yace "Baby plss ki daure ki fito yau mana, i want to see you" ta kalli agogo taga har tara da rabi tace "But baka kalli agogo ba koh doctor" yace "Na kalla mana ai ba dadewa xa kiyi ba" xata yi magana yace "Plssss" kamar xata yi kuka tace "Doctor....." Yace "Plss" turo baki tayi tace "Na ji" daga haka ta katse wayar, tayi tagumi, can ta mike ta dau hijab ta sa ta kashe wutan dakinta ta fita, ko blessing dake daki bata sani ba, tana isa gidan bata gansa parlor ba, ta bata fuska tana kallon kofar daki, a bayanta taji sa a tsaye ta juyo da sauri ya wara mata ido yace "Welcome..." Tace "Toh kiran meye" kama hannunta yayi ya shiga da ita kitchen yace "Am hungry kuma potato and egg nake son ci, hope Mumy baxa ta neme ki ba" shiru tayi bata ce komai ba, can a hankali tace "Ohk... Mumy ta tafi church" Yace "Good, cire hijab din" tace "No xan yi a haka" gun da potatoes suke ta nufa ta debi wanda tasan xai yi masa ta fara ferewa da peeler, cikin kankanin lkci ta gama, duk yana tsaye yana kallonta, kafin minti goma har ta gama, ta daura ruwan Lipton ta juya tana kallonsa tace "Ko baxa ka sha ba" yana rungume da hannunsa yace "Xan sha mana" kayan kamshi ta xuba ta rufe snn ta dau dankali da kwan ta fita ta kai parlor ya bi ta da kallo, tana dawowa kitchen din tace "Toh kaje ka ci kafin ruwan shayin yayi" ya girgixa kai yace "No xan taya ki jira a nn" murmushi tayi bata ce komai ba, haka suka ta tsayuwa har ruwan ya tafasa ta juye flask snn suka fito, sai da ya tilasta ta suka ci abincin a tare, nan ya sa masu film a system tun tana cewa ita gida xata wuce har ta hakura tana kallon, kamar ance ta kalli agogo taga sha biyu saura 'yan mintuna, xaro ido tayi tace "Na shiga uku, doctor kalli agogo" mikewa take son yi ya riketa yace "But it's late Samha...." Turasa tayi tace "Let me plss, ni bana son kana min irin haka, you are just letting me betray my parent, ni ka sake ni" a fusace tayi maganar ta mike ya bi ta da kallo har ta isa kofa ta dawo don daukar takalmanta dake bakin kitchen, lkci daya aka bude kofar parlon, still tayi a gun tana kallon kofar, Ramla, Khaleesat, da Ilham ne suka shigo a tare, juyawa yayi shi ma yana kallonsu sannan ya kalli agogo da mamaki, ko kadan bai lura da abinda ke hannunsu ba da mamaki yace "Lafiya?" A tare duk suka bude murfin ruwan gora me sanyi dake hannunsu suka tuttula masa gaba daya a jiki lkci daya suka ce "Happy birthday....." Bai gama recover ba duk suka fice da gudu suna dariya, me Samantha xata yi banda dariya, ya kalli system dinsa da aka yi masu wankan tare ya mike da gani kasan ransa ya gama baci ya shige bedroom, Samantha ta langwabar da kai ta karasa parlon ta dau system din ta kashe ta ajiye kan kujera a bude, snn ta dauke lallausan rug din da ya jike ta fita da shi waje ta shanya, ta koma kitchen ta dauko mop da bucket ta share ruwan da ya malala a parlon bbu bata lkci ta gama ta wanke mop din, ta dawo parlor tayi jim, can ta kalli agogo sai kuma ta nufi bedroom din, xaune ta gansa gefen gado ya rike kai, ta xaro ido tace "Baka cire kayan ba?" Bai tanka ta ba haka yasa ta karasa ta durkusa gabansa tace "Doctor...." Ganin bai dago ba tayi shiru tana kallonsa, a hankali ta dago kan nasa suka hada ido, kamar xata yi kuka tace "Toh ka cire kayan kar sanyi ya kama ka mana" unbutton din shirt din ya fara yi, ta mike tsaye ta taimaka masa ta cire, tana kallon singlet din jikinsa tace "Toh ka cire doctor" mikewa yayi ya bude closet ya fiddo wasu inners ya shiga bayi, ba a dau lkci ba ya fito, a hankali ta juya masa baya, ya fiddo pyjamas dinsa ya saka, ita dai tana tsaye tana fidgeting din fingers dinta, kamar ance ta juyo ta ga belt hannunsa ya nufi kofa, da sauri ta bi sa ta rikosa tace "No doctor daga suna maka wasa, they just wished you happy birthday, kalli fa hana idonsu bacci suka yi har sae da sha biyu yayi, kai baka san wasa ba?" Ya wani hade rai yace "Ina wasa da su ne xasu xuba min ruwan sanyi a jiki" bata fuska tayi tace "Toh meye don sun xuba ma ruwan sanyi, after all they wished you a happy birthday" karamin fridge din dake dakin ya nufa ta bisa da kallo ya bude ya ciro ruwa me sanyi ita dai kallonsa take taga ya nufota yana bude ruwan, wani k'ara tayi xata gudu ya cafkota, ta kwala wani k'aran jin ruwan sanyi, k'adan ya xuba mata ya ajiye, ta fashe da kuka ya wara mata ido yace "Happy birthday...." Kwace kanta tayi xata fita ya rungumota yana dariya yace "Ashe ba dadi" dage hijab dinta xai yi ta rike da sauri tace "Bana so...." Da karfi ya cire hijab din ya ga yar fingil rigar bacci ne jikinta, ya ja ta xuwa kan gado ya kwantar da ita ya rufa mata bargo murya can ciki yace "Go to sleep it's late" daga haka ya fita ya rufe kofar parlor ya dawo, a rufe ya ga idonta ya dau blanket ya xaga inda take ya durkusa cikin sanyin murya yace "Happy birthday wife!" K'in bude ido tayi duk da tana jinsa, xae mike yaji murya can kasa tace "Happy birthday also dear...." Murmushi yayi ya mike ya kashe wutan dakin ya fita parlor yayi kwanciyarsa. *Haske writers asso*📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 23..... Da asuba ya rakata har gate dinsu don tace karfe bakwai Mumy xata dawo, ya rungume hannayensa yana kallonta yace "dont forget karfe shidda plss love..." Ta kallesa tace "Nace maka ni ban san yanda xanyi ba fa, Mumy xata tambaye ni inda xan je, idan nace mata church nasan ita ma xata je idan bata ganni ba kuma sai in ce me" yayi shiru yana kallonta, can yace "Toh kice mata gidan kawar ki xa ki je mana" turo baki tayi tace "Allah yasa ta bar ni" daga haka ta d'aga masa hannu ta shiga gida. Har bayan la'asar Samantha tunanin me xata ce ma Mumy da xata bar ta ta fita take, can dai ta dau shawarar sa na cewa tace gidan kawarta xata je, ae ko biyar da kusan rabi ta shiga dakinta ta sameta ta xauna gefenta a hankali tace "Mumy xan je gidansu Victoria kinga ta daina xuwa nan don bana xuwa gidansu...." Tsit tayi tana mamakin kanta don ita dai tasan bata karya gashi yau Abuturrab yasa tayi, duk jikinta yayi sanyi ta fara wasa da fingers dinta, Mumy dake mata wani kallo don taga alamar karya take wanda hakan ya daure mata kai wai yau samantha ce ke kkrin hada karya, bata dai nuna ta gano ta ba tace "Tun safe kina gida baki ce xa ki ba sae da yamma tayi?" Shiru tayi bata ce komai ba, Mumy tace "Toh tafi kar ki dade amma" Samantha ta kasa cewa komai kuma ta kasa kallonta, can dai tace "Toh Mumy driver ya kai ni" Mumy ta xuba mata ido sai kuma tace "Toh kije kiyi masa magana" mikewa tayi ta fita ta koma dakinta, hawaye ya cika idonta ta rasa dalili, wayarsa dake gunta ta dauka ta kirasa, yayi mamakin ganin kiranta ya dauka yace "Wife!" Hade rai tayi tace "You made me lie to my mum, ni bana karya kasa nayi karya" sai kuma ta fashe da kuka, yace "Alryt, shknn yi xaman ki a gida kawai, it's nothing and i don't want you to lie because of me" daga haka ya katse wayar, jikinta yayi sanyi ta sake kiransa ya ki d'agawa, ta fashe da wani kukan ta xauna gefen gado, can kuma ta mike kamar mara laka ta shiga bathroom, wanka tayi ta fito ta shirya cikin abayarta tayi rolling, sosai tayi kyau duk da bata yi wani kwalliya ba, ta boye wayarta a jaka ta fito tana rike da jakar, Mumy dake shirin fita church tayi ma sallama ta fita driver ya ja ta xuwa inda tace wato gidansu Victoria, mintin ta sha biyar a gidansu Victoria ta sake kiran Abuturrab, wnn karan sai da ya kusa katsewa ya dauka, kasa cewa komai tayi amma kiris ya rage ta fashe masa da kuka, shi ma dai kamar baxae ce komai ba sai kuma yace "ya aka yi samha?" Ta fashe da kukan da ke cin ta tace "Bayan kasa na fito gida shine ka ki daga kirana koh?" Da mamaki yace "kin fito da gaske? Kina ina" cikin rawar murya ta gaya masa, ya lumshe ido yace "Alryt, gani nan xuwa am sorry plss" daga haka ya katse wayar, shidda da 'yan mintuna ya iso anguwar, tun da ta fito gate yake kallonta har ta karaso ta bude gaban motar ta shigo, ya lumshe ido yace "Am sorry samha" bata ko kallesa ba ya tada motar suka bar gun, wani babban gun make up taga yayi parking, ta kallesa tace "Me xa mu yi a nan?" Ya fito daga motar ya zaga ya bude mata ta fito tace "Me xa mu yi a nan mana" Yace "Follow me ko kuma in kama hannun ki" daga haka yayi gaba ta bi bayansa kamar xata yi kuka, babba ne gun kwalliyan sosai, har kunshi ana yi da gyaran gashi, matar dake gun da alamar ita ce me gun tayi masu sannu da xuwa da fara'a ya nemi kujera ya xauna, Samantha ma ta xauna sai dai duk gabanta faduwa yake, Abuturrab yace "Madam light make up nake son ayi mata...." Samantha ta hade rai tace "Make up kuma!" Bai kalleta ba yace "Xan je in dauko kayanta yanxu...." Matar tace "Muna gyaran gashi da kunshi na amare, bari in kawo maka list ka ga bbu abinda bama yi a nan" Abuturrab yace "No ba sai an kawo ba, a gyara mata gashi kawai sai make up" daga haka ya mike yana ma Samantha wani kallo da manyan sexy eyes dinsa har ya fita, ji tayi kamar ta rusa kuka, nan matar da yaran gun suka taho don yi mata abinda yace. Sai bayan magrib ya dawo rike da leda ya mika ma matar yace "A dan yi sauri madam lkci ya wuce" babu yanda samantha ta iya haka ta bi matar. Gown ce me d'an karen kyau ja with long sleeves, mai ratsin silver daga saman wuyar kawai, dama gata fara gown din ya wani haska ta sai ka rantse amarya ce, gashi kamar an auna ta, ya fito mata da shapes dinta tun daga sama, tayi kyau iyakar kyau, ga gashinta da aka gyara mata bakikirin da shi ya xubo har kasan wuyarta, matar sai maa sha Allah take cewa tana kallonta, necklace ta sa mata da earrings suma silver sai bracelet da wristwatch, ta fiddo takalmi me ratsin ja da silver ta bata ta saka, matar da samantha ta gama tafiya da imaninta tace "Ya sunan ki 'yan mata?" Samantha ta sunkuyar da kai a karo na farko da taji wani iri tace mata sunanta Samantha, murya can kasa tace "Samha!" Matar tace "Ki gode ma Allah Samha kina da kyau, wanda ya xo da ke shine angon naki koh?" Samantha ta sunkuyar da kai kawai, matar tace "Allah sarki, Allah ya bada xaman lafiya da xuri'a dayyaba...." silver head tie mara nauyi matar ta daura mata, sannan ta fesheta da turare kala hudu da ya saka cikin kayan, matar takara mata da nata, snn ta kama hannunta suka fito, tun da suka fito Abuturrab ke kallon Samantha ko kiftawa babu, ita kam kasa dago kanta tayi, duk occupant din wajen kallonta suke ko wanne na fadin maa sha Allah, Har gabansa matar ta kai ta, sai a snn ya mike da kyar ya sa hannu a aljihu ya ciro dubu talatin din dake ciki ba tare da yace komai ba ya mika mata, farin ciki ya lullube matar ganin tulin kudin, karfin halin kama hannunta yayi suka fita tana binsa duk jiki a sanyaye, suna shiga mota ya kamo hannunta cikin raunin murya yace "promise to be with me no matter the situation we re going to find our self samha..." Kasa cewa komai tayi hawaye ya cika idonta, harde hannayensu yyi cikin sanyin murya yace "Talk plss Samha," rungumesa tayi cikin rawan murya tace "I promise!" Kiss ya shiga yi mata a wuyarta, duk ta rikice tana turasa, da kyar ta samu ya saketa, ta hade kanta da gwiwa, jiki a mace ya tada motar ya ja suka bar wajen, sai da ya je gidan wani abokinsa don shiryawa shi ma, sai dai bai bari ta fito ba ya shiga gidan, ba a dau lkci ba ya fito sanye da suit dinsa na royal blue. Bata bari sun hada ido ba har ya ja motar. Wani lafiyayyen hall taga sun yi parking, tun daga waje kana iya ganin uban motocin dake Parke ga abokansa na hannun dama na jiran isowarsa, yana fitowa ya xaga ya bude mata ya kama hannunta ta fito, wani kallo suka dinga mata gaba dayansu shi dai yana rike da hannunta har ya iso gabansu, sai a snn suka ankare, kusan dukkansu suka sa hannu aljihu suka fiddo sabbin dari biyar biyar suka watsa masa shi da ita, lkci daya suka ce "Happy birthday Aliyu" dariyar yake yayi ya na rike da ita ya nufi hall din suka rufa masu baya. Sai ka rantse d'an sarki ko d'an shugaban kasa ke birthday tsabar cika da haduwar wajen don Aliyu akwai son life, manyan 'yan mata da samari masu ji da kai ne kuma a gun, Gaba daya kallo ya koma kan Samantha, wanda hakan yasa Abuturrab ya ji wani kishi ya rufesa, komai da aka yi design a gun red and silver ne, manyan cake har uku ne a gun, nan aka fara shagalulluka, ita dai Samantha taki sakin jiki, shi ma kuma bai takurata ba, Saudat na daya daga matan da suke gun, sai dai tun da ta kyallara ido taga Samantha hankalinta ya tashi barin da taji wai birthday mate dinsa ce kuma da dukkan alama budurwarsa ce, bbu wanda ya dauko Samantha Christian ce, Abutuurab dai na ta kallon agogo don bai son su wuce tara gun, ko da xa su wuce hakan ma yafi son ya maida Samantha gida, tunda Samantha ta xauna bata tashi ba sai da aka fara hotuna shi ma kuma tilasta ta yayi, ae ko kowa so yake suyi hoto tare, har dai aka gama sai yanka cake, Yayi ma abokinsa magana cewar ya ba ma Dj umarnin kashe wakar da ke tashi coz he wants silent, cikin kankanin lokaci gun yayi tsit, wanda hakan yasa kallo ya dawo kan Abuturrab dake facing din Samantha, kasa kallon cikin idonsa tayi, da mamakinta da kowa na gun sai gani suka yi ya durkusa a hankali on his kneel ya sa hannu a aljihu ya ciro wani box me bala'in kyau ya bude, sai ga kyallin diamond, abokansa na ganin haka suka dauko Mp xuwa inda suke ko wannensu na cewa waowww, Abuturrab ya ciro ring din ya kamo hannunta cikin sanyin murya yace "Will you marry me plss?" Tafi hade da ihu ya kauraye ko ina, tuni aka fara video da waya, bbu wanda abun bai burge ba a wajen sai saudat da taji kamar xuciyarta xai fashe, samantha kam hawaye ne ya cika idonta, ta kasa ce masa komai ga ido da ya tsare ta da, da kyar ta gyada kai hawayen idonta ya xubo, cikin sanyin murya tace "Yyess i will!" Dai dai lkcn da ya gama xura mata xoben ya mike ya rungume abarsa, aka dinga tafi da shewa ana daukarsu photo, juyawa saudat tayi ta fice daga hall din da gudu, gift ba na wasa ba Samantha ta samu a gun don har ta fi uban gayyar samun kyauta, karfe tara kuwa ya fita da ita daga gun, duk taki yarda su hada ido, sai da ya kai ta part dinsa ta canza kaya snn ya rakata har kofar gidansu, bata yi wata wata ba ta shige ta bar sa a tsaye, yayi murmushi ya juya ya bar wajen. Xaune taga Mumy a parlor fuskar nan nata bbu alamar rahama, jikinta yayi sanyi ta karasa ta gaisheta kanta a kasa, cikin kakkausar murya Mumy tace "Daga ina kike Rebecca?" Gabanta yayi mugun faduwa tana kallon uwartata a hankali tace "Birthday Mum" Mumy ta mike tace "Birthday din wa" sunkuyar da kai tayi xuciyarta na bugawa tace "A frnd" fincikota Mumy tayi tace "ki gaya min meye hadin ki da likitan dake xuwa gidan nan?" Sosai samantha ta tsorota kafin tace komai uwar ta sauke mata mari cikin tsawa tace "Baxa ki bani amsa ba??? Uban meye tsakanin ku, a ina kika san shi? Har ya sauke ki a mota" Samantha ta fashe da kuka jikinta na rawa tace "Mumy kiyi hakuri don Allah, he's a frnd!" *Haske writers asso*📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 24..... Baki uwar ta bude da mamaki tace "Rebecca yaushe kika fara karya?" Durkusawa samantha tayi cikin kuka tace "Plss Mumy kiyi hakuri am not lying frnd dina ne" Mumy tace "A ina kika san shi?" Rasa abinda zata ce tayi hawaye na sakko mata tace "Kiyi hakuri Mumy" hankada ta tayi cikin tsananin fushi tace "Baxa ki bude baki ki min magana ba?" Jikinta na rawa tace "Watarana ne naje birthday din Suzan shine muka hadu, he helped me" tafe hannu uwar ta shiga yi cikin tashin hankali tace "Nashiga uku, Samantha dama abinda kike yi knn yanzu ban sani ba, when did you change, meye hadin ki da musulmi daga fara bin sa har ya koya maki karya," a fusace uwar ta kuma kai mata mari ta fixgota tace "Maza wuce ki hada kayan ki yanxun nan, dole ki bar gidan nan gobe gobe, baxan bari ki ja mana abun kunya ba, tunda har ya koya maki karya ban san nan gaba me xae faru ba kuma" daga haka ta ja ta xuwa daki, tana tsaye tasa ta gama hada kaya ta tabbata bbu wani abu da tasa a jakar banda kayanta don har wayarta da bata fiye amfani da ba ta karbe, wayar Abuturrab ne dae bata san da shi ba, bedroom dinta ta kai ta ta kulle ta sauko kasa tana huci tana tunanin ghana kawai xata turata gobe tunda tana da visa, Samantha ta hade kai da gwiwa ta dinga kuka, duk ta rasa me ke mata dadi, kallon fingers dinta tayi da sauri taga ring din da Abuturrab ya sa mata na nan, cirewa tayi ta wurgar ta kuma fashewa da kuka, tayi mai isarta ta kwanta nan kasa ta lumshe ido, har ta fara bacci kamar warce aka tsikara ta mike da sauri, kalle kallen dakin ta fara yi tana neman xoben, can ta mike ta nufi ta inda ta wurgar bata gani ba, jikinta yayi sanyi wasu sabbin hawayen suka xubo mata, a hankali ta dinga bin ko ina na dakin tana dubawa, har bayan minti talatin bata gani ba, hankalinta ya tashi ta fara dage komai tana dubawa, kan kace me duk ta juya dakin upside down, da kyar ta ga xoben a wani lungu, ta karasa da sauri ta dauka, dai dai nan aka bude kofar dakin, Mumy, da aunties dinta har uku suka shigo dakin, daya kanwar mahaifinta ce, biyu kuma kannin Mumy ne, Mumy da ta hango xoben dake kyalli hannunta ta karaso da sauri tace "Meye wannan hannunki?" Kasa cewa komai samantha tayi tana kallonsu xuciyarta na bugawa, Mumy ta kare ma dakinta kallo tace "Ubanki kike nema kika rikita min daki, xoben meye wnn kamar na diamond a hannunki" sauke idonta kasa tayi hawaye ya silalo idonta, daya daga aunties din nata a fusace tace "Amma Rebecca ba kurma bace ba dai koh!" Ta fashe da kuka cikin rawar murya tace "Mumy shi ya bani" dafe kirji Mumy tayi cikin tashin hankali tace "Amma na shiga uku ni Rachael, na meye?" Ta sulale nan kasa ta kuma fashewa da kuka sosai tace "He said he wants to marry me" wani jiri Mumy ta dinga ji har sai da Anty Vivian ta riketa, Mumy ta fashe da kuka sosai tace "Ae ni nasan na shiga uku, amma Allah ya tsine ma mutumin nn yar tawa xae yi engaging? Wayyo Allahna kila ma asirce min ita yayi, shi yasa jinina bae taba haduwa da musulmai ba, mugaye ne, matsafa ya ma 'ya ta tsafi, ku kira min David yaji abinda yar sa ta koma, tuni Rebecca ta daina xuwa church na lura, ko taje kuwa bata dadewa take dawowa, Rosary da na bata ta saka sai ta cire, ta bar karanta Bible, ta yaye catechism da dadewa, addu'ar safe yanxu bai dameta ba, kai bata ma yi, Samantha da ko kasheta xaka yi baxata maka karya ba ita ce yanxu da masters a karya, snn ace bae asirce min 'ya ba... Babban abinda ya kuma tada min hankali nayi ta leke ina jiran in ga ta inda xata billo shine yau fa birthday dinta amma yar nn daga ni har babanta bbu wanda tace ma komae abinda bai taba faruwa ba tsawon rayuwarmu tare, ashe birthday d'an iskan ya hada mata" Tana kai wa nan ta kuma fashewa da kuka sosai ta daura hannu a ka, Wani wawan mari kanwar Abba ta dauketa da shi cikin tsananin fushi tace "Waye shi? A ina kika sansa, d'an wani anguwa ne? Me garesa da har ya burge ki kike kulasa?" Kasa cewa komai Samantha tayi sbda wani jiri da ta dinga gani tsabar shigarta da marin yayi, Anty vivian ta rike Sarah kanwar Abba ganin wani marin xata kuma kai mata tace "Haba sis sarah mu bi ta a hankali mana..." Sarah tace "Xaman ta ya kare a Nigeria, gobe gobe xata wuce Ghana, har mu xata dauko ma abun kunya, me xa ayi da musulmi? Yesu yayi mana tsari...." Samantha bata san lkcn da cikin kuka tace "Toh su musulman ba mutane bane? Ina ce Grandfather na har ya mutu musulmi ne shi, kuma dama ba Jehovah ne ya halicce mu gaba daya tare da su ba, kowa da nasabarsa gun Allah.... Kuma a Bible ae dama ance addini xai kasu....." Mumy bata jira jin karashen ba tayi kukan kura sai a kanta, tana duka Sarah na duka, ita kanta Vivian wnn karan wani wawan hauri ta kai mata tana cewa "Rebecca mu kike gaya ma haka???" Da kyar Anty Mary Ann ta ja samantha suka bar dakin, ta shiga da ita wani dakin ta rufe da makulli, Samantha ta sulale kasa ta hade kanta da tiles din dakin, Anty Mary da damuwa tace "Rebecca waye wnn mutumin, meye hadin ki da shi?" Kasa cewa komai Samantha tayi idonta a rufe, xama Anty Mary tayi gefen gado tayi tagumi, tana jin su Mumy na bubbuga kofa kamar xasu cire suna kunduma xagi, daga karshe suka gaji suka bar wajen, Samantha ta mike da kyar ta hau gado ta rufe ido, Mary da ta bi ta da ido ta girgixa kai cike da damuwa, har karfe sha daya samantha bata bude ido ba sai dai ba bacci take ba, mikewa Mary tayi ta shiga bayi, samantha ta juya a hankali taga ta rufe kofar, mikewa tayi ta sauka daga kan gadon da sauri ta bude kofa a hankali kamar kiftawan ido sai ga ta downstairs, Blessing na xaune parlon tana ganinta ta mike da damuwa tace "Sister Rebecca ina xa ki kuma, you re in trouble plss kar ki fita" Hawaye cike idonta tace "Plss don't say anything, kawai kice baki gan ni ba" daga haka ta fice da gudu jin budewar kofa a sama, Blessing ma ta shige kitchen da gudu, ko takalmi bbu kafarta ta fice gidan gaba daya, ae ko Mary na jin budewar kofa ta fito da sauri, ganin dakin wayam ta fice waje dai dai lkcn da Mumy ma ta fito da su Sarah, Mary ta fara kalle kalle hankali tashe, Mumy na ganin haka ta daura hannu a ka ta fara sauka stairs tana cewa "Ae ni shknn na shiga uku na lalace, gudu tayi...." Duk suka bi ta hankali tashe, Mumy ta dinga kwala ma Blessing kira ta fito da sauri, A tsawace tace "Ina Rebecca?" Girgixa kai tayi a tsorace tace "Madam ni a kitchen nake ai...." Kamar Mahaukaciya Mumy ta fita parlon ta dinga kwala ma inusa mai gadi kira ya fito cikin tashin hankali tace "Inusa Samantha ta fita ne?" Inusa yace "Ehh yanxun nan ta fita..." Da gudu su Anty sarah suka fice don bin bayanta, a tsawace Mumy tace "Me yasa ka bar ta ta fita?" Mai gadi yace "Madam ae ba yau ta saba fita ba, in dai xaki kwana church yawanci bata kwana a gidan nan sae asuba take dawowa, nayi xaton yau ma kinje kwana a church ne...." Wani kara Mumy tayi ta daura hannu a ka tace "Yesu!! Ae ni nace dama na shiga uku, Rebecca bata kwanan gida, ina take kwana" kuka sosai ta fashe da, daga haka ta bi bayansu Sarah ita ma da gudu, yau kam samantha bata ji tsoron karnukan dake haushi ba, neman tsoron ma tayi ta rasa, gudu kawai take don tasan da wuya idan ba a san ta fita ba yanxu, tunanin hakan yasa jikinta ya dau rawa a xuciyarta kuwa addu'a take Allah sa Abuturrab bai rufe gate ba, don tasan idan ta tsaya bubbugawa xa a iya risketa kuma tata ta sameta knn gun su Mumy..... *Haske writers asso*📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 24/25 Tana isa gate din ta turasa taji a rufe, kasa bubbugawa tayi sai haki take, hasken torchlight ta dinga hangowa daga nesa, ae bata san lkcn da ta fara buga gate din ba, Abuturrab dake xaune ya rike kai a parlor don ya rasa me ke damunsa tun bayan dawowarsa gida ya mike da sauri kamar dama jiran buga gate din yake ya fito ya karasa ya bude, yana ganinta kuwa ya jawota ya rufe gate din gam, sulalewa kasa tayi, ya bita da sauri hankali tashe yace "What Happened Samha?" Mikewa tayi da sauri ta shige parlor ya juya ya bi bayanta, xaune tayi parlon ta hade kai da gwiwa ta dinga rusa kuka, wani mugun tashi hankalinsa yayi, ya dagota yace "Don Allah ki min magana...." Bai rufe baki ba yaji ana bubbuga kofa kamar xa a cire, mikewa yayi da sauri ta rikosa cikin rawan murya tace "Plss kar kaje, Mumy ce..." Kallon mamaki ya dinga mata, lkci daya jikinsa yayi sanyi, su kuwa basu fasa buga gate din ba, ga haushin da karensa ke yi duk ya cika gidan, to bai son a ji a cikin gida, ya durkusa cikin kwantar da hankali yace "Look Samha, bari in je, nasan me xan yi, tashi ki shiga daki" cikin kuka tace "Don Allah kar kaje plsss" rike hannunta yayi yace "Noo, yanxu xa ki ga soldiers din cikin gidan nn sun yo nan, i don't want that, nace maki nasan abinda xan yi" kasa cewa komai tayi sae dai duk jikinta rawa yake, ya mike da sauri ya fita, ae ko sae ga soldiers har uku suna tahowa, ya d'an kallesu yace "No, it's nothing, kila emergency ne, kuyi wucewar ku kawai..." Juyawa suka yi gaba daya sae da suka sha corner, snn ya isa cage din karensa ya bude, karen ya fito kamar jira yake ya nufi gate din, Abuturrab ya bi bayansa, lkci daya ya bude gate din amma ya tare yanda karen baxae iya fita ba, yamutse fuska ya dinga yi kamar mai bacci yace "Any problem??" Bai gama rufe baki ba Mumy ta cakumosa tana haki tace "Ka fito kin da 'ya ta kar in cinna ma gidan nn wuta yanxun nn, fito min da 'ya ta nace!!" Wani kallo ya dinga yi mata yace "Ban gane ba" wani ihu tayi tace "Baka gane ba koh, to wllh yau sae na tara maka jama'a bring out my daughter oo" A fusace Sarah ta bankesa xata shiga gidan, ya hankada ta waje, daga haka ya matsa karensa ya fito ya dinga wani irin haushi yana tsalle duk suka koma baya da gudu sai dai fa hakan bae sa Mumy ta rufe baki ba, duk ta xama kamar wata xautatcciya, can ta fashe da matsanancin kuka tace "Yesu what have i done to deserve this, why my daughter, why rebecca..." Vivian ta dinga jan ta tana cewa "Sister Rachael mu je kawai gobe sae mu je station kinga karen nn sae ya iya cizan mu" da kyar suka ja ta tana kuka sosai ganin kare fa ya dage xae yi cixo don ma Abuturrab na kiransa, suna barin wajen karen ya dawo Abuturrab ya jawosa ciki snn ya rufe gate, ya shiga parlor ya sa key, duk jikinsa yayi sanyi ya karasa bedroom, xaune ya ganta a kasa ta hade kai da gwiwa tana rusa kuka, durkusawa yayi gabanta cikin sanyin murya yace "Am sorry samha, forgive me plss, i know i caused everything" k'in dago kanta tayi, yayi shiru ya ma rasa abinda xai ce, can ya mike duk jikinsa a mace ya shiga bathroom, ruwan dumi ya hada mata ya fito da towel ya durkusa gabanta yace "Plss ki tashi kiyi wanka sai ki kwanta, you will feel much more better" ganin ba kulasa xata yi ba ya dagota ta fashe da wani kuka mai ban tausayi, bai san lkcn da ya rungumeta ba yace "Noo plss samha, you re making me feel guilt inside me..." A hankali ta dinga kukan ya dagota ya cire mata dankwalin abayar kanta, snn ya daga Abayar ta sauke da sauri, murya can kasa yace "Toh tafi bayi ki cire..." Kamar iska xai hurata ta mike sae kuma ta bude tafin hannunta har lkcn xoben na nan, bata bari sun hada ido ba ta saka a finger dinta ta nufi bathroom din a sanyaye, bayan minti kusan ashirin ta fito daure da towel, gaba daya ta mance da ganinta kasan she's not her self, suna hada ido ta kalli towel din ta juya da sauri, bin ta yayi yace "Noo, kar ki maida kayan ki, i wil give you another..." Rigar Pyjama dinsa ya dauka ya kai mata snn ya fito, goge jikinta tayi ta saka rigar da ya sauko mata har kasan cinya snn ta fito, taga baya dakin, gashinta ta daura ta kwanta hade da lumshe ido. Rike da cup din tea ya shigo dakin, har ya karaso inda take bata bude ido ba, ya ajiye cup din murya can kasa yace "Samha!" A hankali ta bude rinannun idanuwanta ta kallesa, ya sakar mata lallausan murmushin kwantar da hankali yace "Tashi ki sha tea, it will help" shiru tayi bata ce komai ba kuma bata tashi ba, ya kamo hannunta yace "Kinji?" Mikewa xaune tayi ba tare da ta kallesa ba, ya dau tea din ya mika mata ta karba ta kai baki, da yake shayin bbu wani xafi rabin cup ta sha ta mika masa, yace "No, daure ki shanye don Allah" girgixa kai tayi cikin sarkewar murya tace "Na koshi" karba yayi ya ajiye, ya mike ya nufi gaban mirror ya dauko paracetamol biyu ya dau ruwan goran da ya rage ya dawo ya mika mata, ba musu ta karba ta bude ruwan ta sha maganin ya karbi ruwan ta koma ta kwanta ta lumshe, lullubeta yayi da duvet don Ac'n dakin a kunne yake, ya kusa awa daya xaune kafin ya mike ganin sha biyu ya wuce ya dau pray mata da blanket ya fita parlor. Washegari yana dawowa daga masallaci ya hadu da Mami dake kkrin shiga parlonsa, sosai gabansa ya fadi, ta tsaya ganinsa tace "Sai yanxu ka dawo daga masallacin?" Ya risina yace "Ina kwana Mami" tace "Lafiya lau, su wa ke buga gate jiya Aliyu?" Rasa abinda xai ce mata yayi, duk hankalinsa ya tashi har ta so gano hakan, ganin irin kallon da take masa ya dake yayi ta maza yace "Kiyi hakuri Mami, a nan anguwar suke, emergency ne daya daga yaran gidan basu da lafiya!" Tabe baki tayi cikin nuna rashin gamsuwa tace "Ae tun ba yau ba dama ka iya karya" shiru yayi bai ce komai ba tace "Naga alamar your staying here is doing you more harm than before, bari dae Abban ka ya dawo...." Daga haka ta juya ta bar wajen, ya bi ta da kallo a sanyaye, cikin rashin kuzari ya shiga parlor, ya karasa bedroom ya ganta durkushe jikin gado ta hade fuskarta da gadon, karasawa yayi kusa da gadon da sauri yace "me ya faru samha?" D'ago kai tayi tana kallonsa da idonta da suka tashi da gani kasan ta ci kuka kenan da daddare, ya durkusa kusa da ita da damuwa yace "Samha!" Sauke idonta tayi kasa tace "Addu'a nake" sae a snn hankalinsa ya d'an kwanta yace "Ohk, tashi kije kiyi wanka, but you have to hurry up before daybreak, xamu fita kafin su mum dinki su dawo...." Tana jin haka kuwa ta mike ta nufi bathroom, duk tausayinta ya cikasa, yanxu duk shi fa ya ja mata everything she's going through, kuma ko k'adan bata nuna tana jin haushinsa ba, cikin kankanin lkci tayi wanka ta wanke baki da mouth wash ta fito, taga bbu shi a dakin, ta rakube gefe daya don tasan gaskiyarsa su Mumy na iya xuwa yanxu, shi kam main house ya nufa yaji alamar Mami na kitchen da mai aiki, ya haura sama da sauri ya shige dakinsu Ilham duk sun koma bacci, a hankali ya bude press dinsu yana kare ma kayayyakinsu kallo, ganin kamar samantha ta fi son Abaya ya dau wani well ironed Abaya baki da veil dinsa ya rufe gun, rasa yanda xai fita da kayan yayi kar yaje ya ci karo da Mami, bathroom ya shiga ya dauko towel dinsu ya nannade kayan a ciki ya bude window a hankali ya jefar da kayan kasa, yana juyowa yayi ido hudu da Ramla da k'aran bude window yasa ta farkawa tunda basu dade da komawa ba bayan sun yi sllh, mikewa xaune tayi tana kallonsa ya hade rai yace "Ku baku da aiki sai na bacci ne a gidan nan? Oya duk ku tashi ku fita daga dakin nn, breakfast din ma sae Mami taje tana muku?" Yanda ya buda murya yasa duk sauran suka farka, yasan Ramla na iya leka window idan ya fita don haka sai da ya tabbatar duk sun fita suna turo baki snn shi ma ya fita, da sauri ya xaga ya dau kayan ya koma part dinsa, har lkcn tana xaune ya sameta, ya sakar mata murmushi ya ajiye mata kayan ya nuna mata gaban mirror yace "Ga lotion, body spray, perfumes, ki shirya kafin in fito" daga haka ya shiga bathroom don yin wankan shi ma, ko kafin ya fito har ta gama shiryawa tana xaune tayi jigum, mikewa tayi ganinsa da towel ta fice daga dakin, bai wani dau lkci ba ya fito sanye da kananun kaya hannunsa rike da makullin mota yana kallonta yace "Tashi mu je, idan mun fita sai kiyi breakfast" bata ce komai ba ta bi bayansa, ya nufi gun da motarsa ya ke ya bude mata snn ya xaga ya bude ya shiga driver seat, ya fara warming din motar, kamar wanda ya tuno abu yace mata yana xuwa ya koma cikin gidan, kayan ta na jiya ya dauka har da dankwalin ya saka a leda snn ya fito, ya bude bayan mota ya ajiye ya rufe motar, gate ya bude ya dawo ya fitar da motar, ya kuma fitowa ya kulle gate din snn ya shiga motar ya ja suka bar layin, sai da suka hau kan main road snn ya kamo hannunta yace "Samha!" Bata iya ta amsa ba hakan yasa ya kuma kiranta, ta juyo ta kallesa, yace "Gaya min me ya faru jiya" ganin ta ki cewa yasa bae takurata ba, har sai da suka yi nisa sannan yaji cikin sanyin murya tace "I told Mumy everything" kallonta yayi da sauri yace "Me kika ce mata" tsaf ta gaya masa yanda aka yi jiya bata boye masa komai ba, duk jikinsa yayi sanyi ba kadan ba ya kasa ce mata komai, kuka take a raunane wanda yake jin hakan har cikin xuciyarsa, kasa daurewa yayi, yayi parking ya kamo hannunta biyu cikin sanyin murya yace "forgive me samha, ni na janyo komai, kuma duk hakan ya faru ne ta dalilin son da nake maki, no matter what kar ki guje ni Samha, ban taba yi ma wata diya mace irin son da nake maki ba, baya ga mahaifiyata bbu wata a xuciya ta sai ke, ina son ki son da baxan iya kwatanta maki ba, ki yarda da ni, na maki alkawarin har abada baxan barki ba komin wuya da tsanani.... Kuma kin san alkawari kaya ne, i am not using a sugar quintet mouth on you, i mean all what am saying, it's coming from the bottom of my heart" hawaye kawae take, wanda hakan yasa yaji kamar shi ma yayi kukan, ya hade hannayensu yace "But kema ki min alkawarin baxa ki bar ni ba" bata iya ta bude baki ba banda kai da take gyada masa kawai, sun kusa minti goma a haka kafin yayi karfin halin ci gaba da driving din. Karfe bakwai da kusan rabi mota guda na 'yan sanda suka yi parking kofar gidansu Abuturrab, kusan 'yan sanda shidda suka diro, bude kofar wata bakar mota da yayi ma motar 'yan sandar jagora aka yi, Mumy da su Anty Sarah suka fito da wasu maza har uku, da ganin idanuwan Mumy kasan ba tayi bacci ba daren jiya, bubbuga gate yan sandan suka dinga yi da karfi, kwata kwata Mumy bata san main gate din na ta daya bangaren ba, irin bugun da yan sandan ke yi ya ja hankalin masu gadi a can gate din, suka karaso su biyu duk da kayan sojoji jikinsu, suka bude gate din, kallon kallo suka shiga yi tsakaninsu, wani d'an sanda cikinsu ya fiddo id card dinsa yana nuna masu yace "Inspector Gbenga..." Tun kan sojojin su ce komai sae ga Mami da Ramla, duk suka bata hanya ta dinga bin 'yan sandan da su Mumy da kallo, duk da yanda gabanta ya fadi hakan bai hanata dakewa ba murmushi dauke fuskarta tace "Sannun ku da safiya, Allah dai yasa lafiya!" Mumy ta tabe baki tana girgixa kafa tace "Ae babu lafiya har sai dan ku ya fito min da 'ya ta yanxun nan wllh" da mugun mamaki Mami ke kallonta, inspector Gbenga yace "Muna son Hajiya a bamu dama xa mu shiga gidan nn yanxu...." Mami xuciyarta ke ta bugawa ta matsa da sauri tace "ohh bismillanku" daya daga sojan dake tsaye yace "Kiyi hakuri Hajiya sae mun kira Col mun sanar da shi..." Yan sandan suka ce "Sorry plss amma mu ma a bakin aikin mu muke ae" Sojan yace "Ehh gaskiya knn wnn, amma sai mun kira mai gidan" a hasale Mami tace "Toh me xae yi idan kun kirasa xae hanasu yin aikinsu ne?" Wani inspector yace "Alryt kirasa ku sanar da shi...." Cikin kankanin lkci sojojin suka kira mahaifin Abuturrab dake Port Harcourt a lkcn suka sanar da shi komai, mikewa tsaye yyi daga xaunen da yake yayi shirun kusan second talatin a xuciyarsa kuwa ya nanata Aliyu ya kai sau biyar, can ya gyada kai yace "Alryt su shiga..." Daga haka ya katse wayar yan sandan suka shiga gidan tare da su Mumy, iya bincike duk anyi a gaba daya gidan bbu samantha bbu alamar ta kuma, Mumy sae kuka take tana cewa "Yesu why me, ya gudu min da 'ya na shiga uku, wllh duk inda yake ku nemo sa ya fito min da ita, xan dauresa har sae inda karfi na ya kare, xae san da ni yake..." Mami dai na tsaye gefe duk jiki a mace, lkci daya hawaye ya cika idonta, Ramla da su ilham ma banda kuka bbu abinda suke. Dago kai Abuturrab yayi da sauri jin an dafa kafadarsa yaga Hajiya Mariya ce, da mamaki tace "Tunanin meye haka Aliyu, ga ni ga ka na kira ka ya fi sau uku amma shiru!" Ajiyar xuciya ya sauke ya lumshe ido yace "Mumy jikina na bani there is something happening at home, my heart is throbbing..." Cikin kwantar da murya Hajiya Mariya tace "Kayi addu'a Allah ya kawo komai da sauki ka ji son..." Kai kawai ya gyada mata, tun shigowarsu gidan ya kasa cin komai, samantha kuwa tilasta ta Hajiya Mariya tayi ta yi breakfast daga nan kuma ta kai ta bedroom dinta tasa ta kwanta, tana kwanciya kuwa bacci ya dauketa. *Haske Writers asso*📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 26..... Karfe goma da kusan rabi Abuturrab na kofar gida zaune yana danna wayarsa kiran Abba ya shigo wayar, sosai gabansa ya fadi da kamar baxae dauka ba sae kuma ya daga ya kai kunne yyi shiru, daga daya bangaren Abba yace "Kana ji na, ka taho gida yanxun nan am waiting for you, i mean immediately!" kasa cewa komai yayi jikinsa yayi sanyi sosai, yayi karfin halin mikewa ya shiga gida, xaune ya samu Hajiya Mariya parlor hannunta rike da Hisnul muslim, ya isa gabanta ya durkusa yace "Mumy wai kin ji Abba in xo, ni nasan all is not well tunda har hankalina yaki kwanciya" ita kanta sae da taji hankalinta ya tashi, ya girgixa kai ya daura kansa a kafarta cikin sanyin murya yace "Mumy ni baxan iya rabuwa da ita, ban san irin son da nake mata ba..." Dago kansa tayi taga hawaye idonsa, wanda hakan ya bata mamaki sosai anya ma ita ta taba ganin hawayensa, ta girgixa masa kai tace "Be a man Aliyu, ko kaje yanxu just show you know nothing about her whereabout, ni kuma in'sha Allah i will take care of her a nan, baxan bari taje ko ina ba, tashi kaje tunda yace yana jiran ka" mikewa Abuturrab yayi jiki ba kwari ya fita, har ya isa gida gabansa bae daina faduwa ba, kallon motar yan sandan dake bakin gate har lkcn ya dinga yi, can ya dake ya fito ya rufe motarsa ya shiga gidan, ko kallon yan sandan dake tsaye tsakar gidan bai yi ba ya nufi inda ya hango Abbansa dake tsaye sanye da uniform da gani kasan saukansa knn, Mami na tsaye daga gefensa Ga Mumy da tawagarta da alama shi dae ake jira, yana isa kuwa Abba ya sauke masa lafiyayyen mari ya sunkuyar da kai ya kasa dagowa, cikin tsananin fushi Abba yace "Ina ka kai yar mutane?" Da sauri ya dago yace "Yar mutane kuma Abba" komawa baya yayi ganin Abba xae kuma marinsa, ya xaro ido yace "Bbu wata yarinya dake gu na Abba, gun aiki na fita, i know nothing about any girl...." Cakumosa Mumy tayi cikin tsananin fushi tace "Karya kake munafuki algungumi, gashi har ka koya ma 'ya ta karya, na rantse maku yasan inda take, don haka ya fito mun da ita idan ba haka ba a tada Nigeria, bbu ruwana da waye ubanka, ku fito min da yarinya ta....." Cikin kuka sosai ta kare maganar ta sake sa ta daura hannu a ka tace "Na shiga uku na lalace" Abba ya dinga yi ma Abuturrab wani kallo, Mami kam banda hawaye bbu abinda take, kasa kallon inda Mr David ke tsaye rungume da hannunsa Abuturrab yayi, cikin sanyin murya yace "Abba sharri ake son min, i know nothing about all this, toh ina xan kai yar mutane, xa a iya shiga ciki a duba ko tana nan..." Turasa Mumy tayi tana huci tace "Yesu! Kai baka jin kunyan karya ne, ina ce jiya birthday ka ja ta ku ka je, ina ce jiya ka bata zobe wae zaka aureta, ka mance hanyar jirgi daban ta mota daban, meye ya hada warce ta fito from a very good Christian home da musulmi, bbu hadin ku don haka ka fito min da 'ya ta idan ba haka ba in kashe ka har lahira!" Wani kallo Abuturrab yyi mata yace "Ni xa ki kashe kuma?" Girgiza kai yayi yana kallon 'yan sandan dake tsatstsaye yace "Ko da maganar nan xae kai mu kotu ku xaku xame min shaida kashe ni tace xata yi." Abba ya kalli sojoji uku dake tsaye gun yace "Ku saka min shi a guard room, ko ba shi ya dauketa ba sai ya fadi inda take, idan kuma yaki ba sae ta kashe sa ba ni xan harbe sa...." Ta gefen ido Abuturrab ya kalle sojojin kawai ya tafi kai kansa Guard room din kafin ma su nufo sa, Cikin tsawa Abba yace "Ku bi sa ku sa shi nace" Daga haka ya nufi yan sandan dake gun, Mumy ta watsa ma Mami wani kallo tana hawaye tace "Amma kin haifa ma kanki jaraba, don wnn d'an naki annoba ne a gari...." Vivian ta ja hannunta suka yi waje tana rusa kuka. Har bayan azahar Abuturrab na guardroom daga shi sae singlet da dogon wando, bai wani damu ba don sbda shi ma aka yi guard room din a gidan, don haka inda sabo yaci ace ya saba, ko d'an shekara 15 aka saka a gun sae yaji jiki tsabar k'ankantar gun ga uban zafi, ko kwakkwaran motsi bae iya yi, a takure yake waje daya kansa ma baya iya dagawa straight sae a duke, tun bai kai sha biyar ba Abba ke jefasa nn idan yayi laifi kuma sae yafi awa biyar a haka, rabonsa da guard room tun yana 27 yrs wato 3yrs back da ya dauko wani maganan, karfe uku yaji an bude kofa daga waje, ko ba a gaya masa ba yasan Mami ce don ita kadae ke xuwa idan aka kullesa, ae ko ita ce, ta durkusa ta bude karamin kofar da yake ciki da aka sa ma uban kwado, da ganinta kasan ta ci kuka, kamar jira yake tana budesa ya fito duk ya jike jagab da gumi, kasa kallon idonta yayi, ya dafa gwiwansa kansa a sunkuye don gaba daya jikinsa yayi tsami, ga wuyarsa da ya rike, muryarta yaji tace "Aliyu ina 'yar mutane" bai d'ago ba kuma bai ce komai ba, can dai ya dago da kyar jin tayi shiru, tausayinta yaji sosai shi dai yasan tun da kwakwalwarsa ta fara aiki irin na mutane rabon Mami da samun kwanciyar hankali, ko da yaushe cikin dauko magana yake ba babba ba ba karami ba kuma a kanta komai ke karewa don Abba cewa yake ita ta 6ata shi, kwanan nan ne ma abun ya lafa bayan ya fara aiki don ko lkcn yana sch hankalin iyayensa ba a kwance yake ba, kamar xae yi kuka yace "Mami ni fa ban san komai kan maganar nan ba sae xalina ake ci kawai!" Hawaye ya gani idonta ya xube nan kasa yace "Noo Mami don Allah kiyi hakuri...." Dakewa tayi tace "Ina yar mutane take Ali?" Shiru yayi kafin ya dago a hankali ya goge xufar dake fuskarsa yace "Mami...." Sai kuma yayi shiru, sauke idonsa kasa yayi yace "Tana nan!" Mami ta durkusa gabansa ta dago kansa tace "A ina?" Kallonta yayi murya can kasa yace "Mami.... Mami ita nake so and i want to convert her...." Komawa baya Mami tayi da mugun mamaki tana kallonsa kamar idanuwanta xa su fito, cikin rawar murya tace "Aliyuu!" Marairaice mata yayi yace "Mami ni idan ban aureta ba Allah xan iya mutuwa wllh, i will be nothing without her" hawaye ne ya cika idonsa, wanda rabon ta da ganin hakan tun yana d'an shekara goma, ko me xaka yi masa baxa ka taba ganin hawayensa ba sai dai idonsa yayi jajir kirjinsa yayi ta sama da kasa tsabar dacin rai da rashin ji irin nasa, ya daura kansa a jikinta muryarsa na rawa yace "First love support me plss, i love her, ni baxan iya rabuwa da ita ba, kuma Mami idan na musuluntar da ita lada xan samu fah..." Hawaye kawae Mami take duk jikinta yayi sanyi, ita kam tana ganin jarabawa tun da ta haifi Aliyu, ta saita kanta cikin sanyin murya tace "Toh tana ina?" Da kamar baxae ce komai ba sai kuma yace "Tana gidan Mumy!" Da mugun mamaki tace "Mariya?" Yayi shiru bai ce komai ba, ta sauke ajiyar xuciya a hankali, jin tayi shiru ya dago da sauri yace "Mami plss kar fa ki ce ma kowa haka, don Allah kar ki fadi Mami...." A rude ya kare maganar, cikin kwantar da murya tace "Ka gwammace kayi ta shan wahala knn, to ai shknn, shiru xan yi da baki na idan ma ya kashe ka kai ka ja ma kanka, tashi ka shiga ciki kafin a ganmu dama cewa yake ni ke supporting din ka" kallon d'an kurkukun yayi kafin ya marairaice yace "Mami k'ishi nake ji sosai wllh" mikewa tayi tace tana xuwa snn ta fita, ya fi kowa sanin halin Mami yasan wannan duk pretending take masa, ya kalli bunch of keys din da ta ajiye nan kasa bayan ta bude sa, ya dauka da sauri ya cire biyu ya tona kasa ya boye a cikin d'an room din, yana nan durkushe yana yi yana lekan sojoji biyun dake tsaye waje har ta dawo ya sunkuyar da kansa da sauri, Ruwan babban gora me sanyi ta kawo masa da Hollandia yoghurt, sae dambun nama cike a plate tace toh tashi ka shiga kafin ya yo nan, karban ruwan yayi ya sha kusan rabi, Key din dake ajiye kawae take kallo can ta dauka tana weighing dinsa ta kallesa strictly tace "Ka cire key a nan bani!" Da sauri yace "Key kuma Mami" wani kallo tayi masa tace "mike tsaye" yana tashi ta sa hannu aljihunsa ta dudduba taga babu, ta leka guard room din ma bata ga alamar key ba tace "Toh shiga ciki" ya ajiye ruwan hannunsa fuskar nan tasa kamar xae yi kuka ya durkusa ya shiga ta tura masa abubuwan da ta kawo snn ta rufe gun da kwado ta juya ta nufi kofa, ya bi ta da kallo yana murmushi har ta fita. Ko minti goma ba ayi da fitarta ba yasa key ya bude gun a hankali ya fito, ya dau shirt dinsa dake rataye gun ya kakkabe ya saka snn ya saka takalmansa ya nufi kofa da sauri, lkci daya ya banke kofar ya fice a dari da sittin kafin sojojin su ankara, ae ko suka bi sa da gudu, gudu yake kamar jirgi xae tashi sama, wani soldier ya ciro whistle a aljihunsa ya dinga hurawa, ae ko sae ga sojoji har uku sun fito, Abba ma ya fito balconynsa a sama ya rungume hannu da mugun mamaki yana kallon Abuturrab, komawa yayi don dauko bindigarsa amma kafin ya dawo tuni ya isa gate da karfi ya finciko mai gadin sojan dake bakin gate yana kkrin datse gate din ya wani wurgar da shi ya fixgo gate din ya fice, gudu kawai yake kamar xae tashi sama, wanda hakan ya tsorata mutane duk suka fara gudu su ma, ko kallonsu bai yi ba har ya iso titi ya tsayar da mai adai daita bai jira ya tsaya ba ya afka ciki yace "Mu je muje da sauri....." Mai adai daita ya ja machine dinsa da sauri don shi ma ya tsorata, Abuturrab ya sauke ajiyar xuciya ya share xufar fuskarsa ya bude button din riga. *Haske writers asso*📚✍🏻 It's Khaleesat Haiydar👌🏻 💫 *Noorul Huda*💫 27..... Gani yake kamar ba tafiya mai adai daitan yake ba duk da yasan yayi escaping don baxa ma su san inda ya bi ba, yayi tsaki yace "Malam ajiye ni nan dan Allah" Mai adai daitan yayi parking Abuturrab ya fito yace "Sae dai kayi hakuri bani da kudi" daga haka ya yi gaba da sauri, mai adai daitan ya bi sa da kallo, yanxu kawae so yake ya gansa gidan Hajiya Mariya yasan tun da ya fadi ma Mami kamar an je an dauko Samantha an ba iyayenta ne, makullin motarsa dama tun da aka sa shi guardroom Abba ya karbe da wayoyinsa, wani bike ya tsayar yana kallon mutumin dake kai yace "Ehrm Don Allah malam ka goya ni xuwa Kofar Nasarawa idan ba damuwa..." Mutumin yace "Ba can nayi ba, nama kawo gida ka ga inda xan shiga..." Abuturrab yace "Toh don Allah ara min bike din... Xan dawo maka da shi" wani kallo mutumin ke ma Abuturrab daga sama har kasa baki bude, Abuturrab ya dafa sa yace "Na maka kama da barawo???" Shi dai mutumin kallonsa kawai yake, Abuturrab ya fixge key din yace "Nafi karfin satan machine, kuma i think da wuya a ga barawo Aliyu Haiydar! Sauka ka ban machine malam" kamar soko haka mutumin ya sauka, Abuturrab ya hau ya tada machine din ya figa da gudu ya hau kan titin, alarm mutumin ya saki bayan Abuturrab ya bace masa yana cewa ya hadu da d'an rufa ido. Cikin kankanin lkci Abuturrab ya iso gidan Hajiya Mariya, a sanyaye ya sameta a parlor ya karasa ya xauna yace "Mumy!" Ta kallesa tace "Me kace ma Mami" shiru yayi sae kuma ya mike da sauri yace "Tana ina Mumy?" Hajiya Mariya tace "Kaga ka hada ni da Mami sae da nace kar kace tana nan, to in'sha Allahu nasan duk inda suke sun ma kusa gidan nan yanxu" Abuturrab ya xaro ido ya nufi bedroom dinta da sauri ya samu Samantha kwance amma idonta biyu, ya karasa ya durkusa kusa da ita yace "Xa mu tafi yanxu samha!" Mikewa xaune tayi ya mike ya fita ta bi bayansa, durkusawa yayi kusa da Hajiya Mariya yace "Mumy babu kudi hannu na...." Mikewa tayi cikin harshen fullanci tace ya sameta a daki, bin bayanta yayi ta xauna tace "to yanxu ina xa ku Aliyu?" Ya shafa kai yace "Anywhere mum, kawai ki ban kudi kafin su karaso" Mikewa tayi ta dau purse dinta ta bude tace "Dubu uku kadai ke garen yanxu amma ga atm card!" Duk biyun ta hada masa ya karba, tace "Toh ta ya xan same ka, na kira wayarka duk switch off" yace "Abba ya karbe wayar, ina da number ki a kai i will call you idan na samu waya Mum," Daga haka ya juya ya fice ta bi sa da kallo, can ta fita ita ma, tana kallon Samantha tace "Toh xan kira ku kin ji daughter" Samantha ta gyada mata kai cikin sanyin murya tace "Nagode Mum" daga haka ta bi bayansa, Hajiya Mariya ta bi su da kallo cike da tausayi, suna fita Abuturrab ya kalleta ya langwabar da kai yace "Samha Bike xa mu hau fa!" Ta kalli machine din snn ta girgixa masa kai tace "Ban iya hawa ba...." Dariya ta basa yace "Toh ba sai in daura ki ba" ta koma baya da sauri tace "No ni ban taba hawa ba, bana so" gani yayi lkci xa su bata yace "Toh follow me fast..." Ta bi sa da sauri suka fita, wata hanyar daban ya dauka har suka iso main road ya tsayar da adai daita suka hau, mai adai daitan ya tambayesa inda xa su yace "Mu je gaba kawai" samantha ta kallesa tace "Ina xa mu je" kasa ce mata komai yayi ganin yanda idonta ya fada, ya kamo hannunta a hankali yace "Am sorry for everything samha" bata ce komai ba, ya kalli mai adai daitan yace "Jan bulo xaka kai mu." Suna isa mai adai daitan yayi parking dai dai inda Abuturrab yace yayi, yana sauka ita ma ta fito, ya mika masa dubu dayan hannunsa ya basa canji ya kalleta yace "Mu je" bin bayansa tayi ya kwankwasa gate mai gadi ya bude, suna gaisawa ya shiga gidan ita ma haka, sai a snn a hankali tace "Doctor ina ne nan?" Ya kalleta yace "Gidansu frnd dina ne nan, bbu wayar da xan kirasa shi yasa mu ka xo" Farida kanwar Mujaheed na xaune karkashin umbrella tree da alamar assignment take, tana ganinsu ta mike tace "Lahh ya Aliyu daga ina?" Yace "Mujaheed na nan?" Tace "Ehh yana nan" yace "Kice ina jiransa" tace "Toh" snn ta kalli Samantha tace "Sannu da xuwa" Samantha ta sakar mata murmushi tace "Nagode" daga haka yarinyar ta wuce ciki, ya kalli samantha yace "Mu je ki xauna" bin bayansa tayi suka xauna karkashin bishiyar, ba a dau lkci ba Mujaheed ya fito, ya xaro ido yana kallon Abuturrab yace "Daga ina haka?" Abuturrab bai tanka sa ba har ya karaso ya ja kujera ya xauna yana kallon Samantha murmushi dauke fuskarsa yace "Sannu yan mata!" Samantha ta sunkuyar da kai tace "Ina yini" ya amsa da fara'arsa, Abuturrab yace "Kira farida su shiga ciki, xa mu d'an fita da kai ne yanxu" Mujaheed yace "Ohk" ya ciro waya ya kira kanwarsa ta fito, Abuturrab ya kalli Samantha yace "Samha ku shiga ciki am coming back soon" kallonsa kawae take lkci daya idonta ya kada, mikewa yayi da sauri yace "yanxu fa xan dawo Samha" dago ta yayi suka bar gun daga Mujaheed har kanwarsa suka bi su da kallo, jikin flowers ya tsaya ya daga kanta yana kallon kwayar idonta yace "Ko baki son nan din ne?" Ta girgixa kai bata ce komai ba, a hankali ya kai lips dinsa forehead dinta murya can kasa yace "am coming back soon dear" Daga haka ya kama hannunta suka dawo inda suke ya hada ta da farida suka shiga cikin gidan, A motar Mujaheed suka bar gidan, sun dan yi nisa Mujaheed yace "Kai malam wai ina xa mu" Abuturrab yace "Yi parking muyi magana" Mujaheed yayi yanda yace snn yace "Wnn ba yarinyar nan da ka taba kawowa clinic bace? Dama budurwarka ce?" Abuturrab yace "Ni dai ka saurareni ina son pls ka min wani favour" Mujaheed yace "Na me?" Abuturrab yace "Laifi na yi ma Abba, pls so nake kayi pretending baka san komai ba kaje can gidanmu da sunan kaje daukan ajiyar ka, sai ka duba briefcase a bedroom dina ka dauko min gaba daya Credentials dina, snn akwai atm cards dina har biyu a gaban mirror ka dauko min plss frnd" tun da ya fara magana Mujaheed ya bude baki yana kallonsa, can ya fashe da dariya yace "Me kayi kuma again?" Abuturrab ya tabe baki yace "Oho dai, kawai ni dai nasan tun safe ake cin xalina.... Kaje yanxu plss" mujaheed yace "Abban na gida ne?" Abuturrab yace "May be" Mujaheed ya girgixa kai yace "In dai yana nan baxan iya ba wllh" Abuturrab yace "Oh haka xaka min?" Mujaheed yace "No gaskiya kenan fa, to ita kuma yarinyar nan da kake yawo da fa?" Abuturrab ya shafa kansa yace "Kaga it's a long story yanxu kayi abinda nace idan ka dawo sai in baka labarin," Mujaheed yyi shiru snn yace "Ka fa san halin Dad dinka, xae iya gano hada baki muka yi, why not ka bari da daddare...." Abuturrab yayi tsaki yace "Kai dai kaje ynxu kawai, you have to pretend, sai kace kana ta kiran lines dina basa xuwa, but bani wayar ka daya in case of anything sai ka kira ni" Mujaheed yace "No gaskiya ka bari da daddare?" Abuturrab yyi shiru sai kuma yace "Toh shknn" Mujaheed yace "Da motata xan je?" Abuturrab yace "A'a kawai ka dau tricycle kaga bbu wanda xae xargi komai, kana xuwa kuma ni xaka fara tambaya" Mujaheed yace "Ohk" gidan wani abokinsu suka tafi, suka tsaya har bayan magrib, Abuturrab dai gaba daya hankalinsa na kan Samantha duk da sun yi waya ya fi sau goma ta wayar farida, Bakwai da kusan rabi Abuturrab yace "Toh kaga kar dare yayi kuma Mujaheed ka tashi ka je" Mujaheed yace "Ni dai anya xan je kuwa..." Abuturrab ya marairaice masa, da kyar ya kuma lallaba sa har ya amince daga karshe yace "Toh ina xan sameka?" Abuturrab yace "Ina nan xan jira ka har ka dawo" daga haka Mujaheed ya fita ya dau adai daita ya wuce, Mujaheed na isa yaji gate a kulle wato sai ya xaga ta daya gate din bbu yanda ya iya haka ya xaga, yana shiga ya gaida sojojin dake wajen, sae da gabansa ya fadi ganin Abba a compound suna magana da wani sanye da khaki da alamar abokinsa ne, don compound din akwae haske sosai, yana ganinsu yayi kasa da kai har ya isa gabansu ya risina ya gaidasu, duk suka amsa, Abba yace "Daga ina haka?" Mujaheed yace "Daga gida nake Abba, gun Abuturrab na xo..." Abba yace "Ohk!" Abokin Abba yace "Abuturrab din bai nan ai" Mujaheed yace "Ohk kuma ina ta kiran wayarsa tun rana baya shiga, dama akwai ajiyar da na basa xan karba ne bari in duba ko kofar a bude yake" Abba yace "Ohk" Mujaheed ya sauke ajiyar xuciya ya nufi part din Abuturrab, a bude ya tadda gun ya shiga ya dauko duk abinda Abuturrab yace masa snn ya fito, yayi mamakin ganin sojoji biyu tsaye kusa da balcony sai dai bai ce masu komai ba ya wuce su, yana isa tsakiyar compound ya samu su Abba yanda ya bar su a tsaye ya karasa yace "Abba na dauka xan wuce" Abba na gyada kai yace "Ohk...." Ko rufe baki Abba bai yi ba, Mujaheed ya ji an cafkesa ta baya ya juya da sauri ya ga wani soja ne, sojan ya karbe envelope din hannunsa ya ajiye sa kasa sannan ya fara cajin aljuhun wandonsa ya ciro atm cards din ciki da wayarsa ya jefar kan envelope din, Abokin Abba ya durkusa ya dau Envelope din ya bude ya fiddo abubuwan ciki, banda xare ido babu abinda Mujaheed yake, Abba ya karbi takardun ya kalla snn ya maida dubansa kan Mujaheed, Gyada kai yayi yana wani murmushi ya jefar da takardun kan Envelope din yace "That's a brave play, yeah kun yi kokari daga kai har shi" dukawa yayi ya dau wayar Mujaheed yace "Akwai waya hannunsa ko babu? Kuma kana min karya in sa a kai min kai barrack yanxun nan" Mujaheed da banda xufa bbu abinda ke karyo masa cikin dakiya yace "Ehh Abba akwae daya wayata a gun sa" Abokin Abba na gyada kai yace "Good, kirasa kasa a hands free kace ku hadu a filin polo yanxun nn ya karbi sakon" Da kyar Mujaheed yace "Toh" nn ya shiga kiran daya wayarsa dake gun Abuturrab, Abuturrab da ya fita yana jiransa a mota ya daga kiran da sauri yace "Yane Mujaheed ka dauko?" Mujaheed ya kalli Abba, Abba ya watsa masa wani firgitattcen kallo, da sauri yace "Ehh ehh wllh na dauko! Emm kana ji na mu hadu a filin polo yanxun nn ka karba" Abuturrab yyi shiru, murya can kasa yace "F**k you, ka bari an gano mu knn!" daga haka ya katse wayar ya jefar. *Haske writers asso*📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 28..... Tada motar yyi da sauri tunawa da Samantha da yayi, yasan in dai mujaheed yaga haza to fa xae iya cewa tana gidansu ma, cikin kankanin lokaci ya isa gidansu Mujaheed gabansa na faduwa, kusan a tare suka shiga compound din da kanwar Mujaheed Aysha ta dawo daga makaranta, ya amsa gaisuwarta yace "Kice ma bakuwar da ke ciki ina jiran ta pls hurry" tare samantha suka fito da Farida ta raka su har gun mota ya sosa kai yace "Kice Umma tayi hakuri ina nan xuwa gaida ta, kunya nake ji shi sa ban shigo ba" dariya kawae Farida tayi tace "Ya Jaheed fa?" Abuturrab yace "Ehh yana nan dawowa..." Daga haka ya sa samantha ta shiga mota shi ma ya shiga da sauri, farida ta d'aga masu hannu ya ja motar ya bar layin, yana fita layin motar sojoji na shiga, xaro ido yyi don bai san ko sun gansa ba ya kara gudun tukinsa, sae da suka dan yi nisa ya kalli samantha yaga idonta na waje, wani tausayinta yaji sosai ya kamo hannunta a hankali yace "Samha!" Kallonsa tayi bata ce komai ba, yace "Kin ci abinci?" Kai kawae ta gyada masa, cikin sanyayyen murya yace "Ki kwantar da hankalin ki kar ki sa ma kanki damuwa plss am with you now and forever..." Hawaye ya ga idonta, yayi parking da damuwa yace "Baki yarda da ni ba kenan Samha..." Ta fashe da kuka tace "My parent...." Ya rike hannayenta duk biyun yace "Ni ma na bijire masu duk sbda ke, kinsan irin neman da ake min yanxu? A guardroom Abba na yasa aka kulle ni da safen nan amma sae da nasan yanda na fito, na tura Mujaheed can gidan ya dauko mun Atm cards dina shima yana can nasan an kullesa yanxu kuma nasan xae iya cewa kina gidansu shi yasa na dauke ki, am at risk Samha but i don't care in har ina tare da ke, i love you... I can do anything for your love" hannu yasa ya share hawayen da ke idonta yace "Kar ki damu Allah yana tare da mu!" Sunkuyar da kai tayi bata ce komai ba, ya ci gaba da tukin, a wani atm ya tsaya yace yana xuwa snn ya fita, sae da ya fara duba nawa ne a account din Small Mum din tasa snn yayi withdraw din dubu hamsin, kamar ance ya waiga yaga motar sojoji na kokarin shan cornern gun bank din, da sauri ya koma ya labe jikin Atm din, ta gefen ido yake kallon motan gabansa yayi mugun faduwa ganin abokin Abbansa da ya fito daga gaban motar, sojoji hudu ma suka sauka daga baya, kamar kiftawan ido ya taho a 160 ya shige cikin mota yayi wani reverse bae damu da harbin da suka fara ba, ko kallon titi bai yi ba ko mota na xuwa ya hau titin ya ja motar a guje, Samantha da duk ta gama rikicewa ta dinga kwala ihu a cikin motor, ta madubi ya ga sojojin sun biyo sa a tasu motar da gudu, ya yo waje da ido yace "Kan bala'i" sae ka rantse tashi sama xae yi tsabar yanda yake gudu don ma titin bbu wasu motoci, samantha dake ta rusa kuka sae cewa take don Allah doctor ka tsaya, don Allah ka tsaya, Bai ko kalleta ba bare ya san me take cewa, hankalinsa ya gama tashi ganin sun kusa tadda su a lokacin kuma suna wajajen court road, bai damu da traffic da ya nuna masa green ba ya wani sha kwana da gudu har ya kusa karo da wata mota ya kauce mata ya ci gaba da gudunsa, traffic din nan ne ya taimaka suka samu distance tsakaninsa da soldiers din, sosai ya ga karfin halin samantha don yasan da wata ce da tuni ta suma, har ya hau titin unguwa Uku bai sassauta gudun da yake ba, a can baya sosai yake hango motar soldiers din, bai son ya shiga wani layi su tadda traffic shi yasa ya gwammace yayi ta gudu a express, hankalinsa ya tashi ganin man motan yayi kasa sosai, yana fara fita outskirt din kano yaga da nisa fa sosai tsakaninsu ya ja ya tsaya ya cire makullin motar ya fito da sauri, har lkcn kudin da yayi withdraw da atm card na aljihunsa, ya xaga ya bude inda take ya fito da ita, wani hanya kamar gona ya ja ta suka bi da gudu, daji ya dinga gani sosai a gaba amma hakan bae sa ya dakata ba, ita ko sai kuka take tana cewa "Baxan iya ba Doctor ka tsaya plss" a haka ya ja ta suka shiga dajin, bai damu da thorns din ciki da dogayen ciyayi ba ga uban duhu suka dinga ratsawa a haka, tafiya sosai suka yi a ciki ya ga kamar numfashinta na neman daukewa tsabar gajiya don jan ta kawae yake, rikota yayi da sauri ya nemi karkashin wani bishiya ya xaunar da ita yana kallonta bnda kyallin idonta bbu wani haske da yake gani a dajin, ta rike duk hannunsa biyu da kyar tace "Ruwa xan sha doctor!" Maida numfashi ya dinga yi yana kallonta, can ya runtse ido ya dinga maimaita innalillahi wa inna ilaihi raji'un a xuciyarsa, bude idon yyi ya dafe kansa, ta xame hannunta daga nasa ta fashe da kuka, mikewa yayi yana dube duben inda xai samo mata ruwa yaji ya yi kick din abu, da sauri ya duk'a yana laluba meye wnn yaga kettle ne, da ruwa amma ba da yawa ba a ciki, dagawa yayi duk da bai san ruwan meye ba ya kai baki ya sha yaji dai ruwa ne sai dai da jin sa a baki kasan ba wani mai kyau bane, ya hadiya da kyar snn ya kai mata baki, karba tayi ta sha gaba daya, ya ajiye butan, ta rike hannunsa gam cikin rawan Murya tace "Am afraid doctor, tsoro nake ji" xaunawa yyi gefenta ya jawota jikinsa murya can kasa yace "Don't be, am here to protect you, am with you" shiru tayi tayi lamo a jikinsa wanda hakan yasa ya dinga jin bugun xuciyarta, sun kusan minti talatin a haka taji ya kankameta, ta d'ago da sauri, taga idonsa a runtse, a hankali ya bude yana kallon kasa murya can kasa taji yace "Ant, i think it's an ant" kalle kallen kasan ita ma take, xaro ido tayi tayi wani uban ihu da sai da ko ina ya amsa, sai a snn ya ga me ta gani, wato kunama shi ba babba ba shi ba karami ba, ya toshe bakinta ya sa kafa yayi smashing dinsa, ko ina na jikinta rawa yake ta dinga cewa it's a scorpion, ya kai bakinsa kunnenta yace "Shhhh na fa kashe shi..." Jin baxata yi shiru ba ya lumshe ido ya rungumeta gam, tayi lamo jikinsa, a hankali ya xame dankwalin kanta ya daura a gun da kunaman ya harbesa, ba a dau lkci ba bacci ya dauketa. *Haske writers assoasso*📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 29..... Daren ranan Abuturrab bai rintsa ba, har asuba yana rungume da ita, gari na fara haske ya kare ma dajin kallo, sai yaga ashe gona ce gun gaba daya, bishiyoyin mangoes da lemo ne yasa gun ya xama kamar daji da daddare, ya kalli wani tabarma dake can nesa da su a shimfide da wani sanda, da alamar dae mutane na xuwa gun, butoci har biyu ya gani bayan wanda ya samu ruwa a ciki jiya, kwance dankwalinta dake daure kafarsa yayi ya shimfida nan kasa snn ya kwantar da ita a hankali ya mike, wani mugun ciwon kai ya dinga ji ya taka a hankali har ya isa inda butan yake ya ga cike yake da ruwa ya dauka ya xaga ya daura alwala snn ya dawo, ya kalli gabas ya tada sllh, bai idar ba samantha ta farka, mikewa xaune tayi da sauri tana kare ma gun kallo, a hankali ta mike ta karasa gun butan da ya ajiye ta dauka, kallonta kawae yake bayan ya idar, ta juyo ya sakar mata murmushi cikin sanyin murya tace "I want to ease my self" yace "In raka ki?" Da sauri ta girgixa masa kai yana murmushi yace "Ohk" ya nuna mata inda xata tafi, ta juya ta wuce, ko da ta dawo bata gansa ba, ta fara kalle kalle da manyan idonta, muryarta na rawa tace "Doctorrr" tim taji fadowar mango a sama, ta koma baya a tsorace tana kallon sama ta gansa samar bishiyar yana tsinkar nunannun mangoes, ya kashe mata ido yace "Breakfast...." Daga haka ya ci gaba da tsinkar mangoes din masu kyau har ya tsinko fiye da ashirin, ji tayi ya diro kasa, ya karasa ya dauko dankwalinta ya dawo ya durkusa ya kwashesu, ta karasa inda yake ta durkusa gabansa a hankali ta shiga taya sa kwashewa, ya sakar mata murmushi yace "Bari toh in kara plucking din pawpaw ae kina so" bata ce komai ba ya mike ya isa inda sanda ke ajiye ya tafi gun bishiyoyin gwandan, can ya koma baya ita dae kallonsa kawae take, taku daya biyu yayi ya buga uban tsalle ya doki ripe pawpaw guda daya da sandar hannunsa ya fado, murmushi tayi ta dauke kanta ya dawo rike da pawpaw din yana murmushi ya ajiye mata, xaunawa yayi yace "Tunda bbu ruwa haka xa mu sha mangoes din..." Daga haka ya dau mango daya ya kai baki, dauka ita ma tayi ta kai baki a hankali, biyu kawae ta sha tace ta koshi, yace "Efizzy xa ki min" murmushi tayi ta girgixa kai kawai, duk yanda yayi da ita tasha kin sha tayi wai ta koshi, pawpaw din ma shi kadae ya sha kayansa wai bata sha, yana gamawa yace "We will leave yanxu...." Mikewa yayi ya dau sauran mangoes din da sanda yana rike da hannunta suka fara tafiya can gaba, da sandar ya dinga clearing masu daji don duk a tsorace take duk da kana ganin hanyar ma kasan ana bi sae dai ba sosai ba, tafiya kawae suke har kusan karfe tara ganin ta gaji sosai ya langwabar da kai yace "Ko in goya ki baby" kamar xata yi kuka tace "Doctor wae ina xa mu...." Yace "In da Allah ya kai mu" bata kuma cewa komai ba suna ta tafiya ga uban rana me xafin gaske har sha daya tayi, ta durkusa tana haki tace "Wayyo doctor i can't go futher am very thirsty" durkusawa shi ma yayi cike da tausayinta, ta fada kansa hawaye cike idonta tace "Na gaji, yunwa nake ji" ya rungume ta yace "Kiyi hakuri plss, so nake mu fita dajin nan ne so i will find you something to eat..." murya suka ji bayansu, ta kankamesa a tsorace ya juya yaga wani tsohon bafullatani sanye da katon hat wanda hakan yasa ba sosai yake yake hango fuskarsa ba, hannunsa rike da sanda cikin hausan sa da bai fitowa irin ta fulani yace ma Abuturrab "yarinya me ya kawo ku nan" Abuturrab da yaji sanyi sosai a ransa yace "Mun yi 6atan hanya ne Baffa!" Bafulatanin yace "Subhanallahi.... Ina ne xa ku?" Abuturrab ya sake samantha ya mike yana kallon dattijon cikin harshen fillanci yace "Daga kano muke xa mu kaduna barayi suka biyo mu tun jiya da daddare shine muka yo dajin nan" tsohon ya washe hakoronsa da goro yayi masa destroying da fillanci yace "Dama ina ganin ka nasan kai namu ne, ashe d'an uwana ne, barka da arxiki da barayin basu cutar da ku ba" Abuturrab murmushi kawae yake yana gyada kai, dattijon ya kalli Samantha da yaren yace "Sannu yarinya ta barka da arxiki" Kanta a kasa tace masa sun gode da harshen fillanci ita ma wanda hakan yayi mugun daure ma Abuturrab kai ya tsaya kallonta kamar idanuwansa xasu fito, dattijon yace "Rigar mu na nan kusa ku taso mu je ku huta, tafiyar minti talatin ne xae kai mu can, na fito kiwo ne dama na hango ku nayi xaton barayin daji ne, ga can inda na boye shanaye na" dariya Abuturrab yayi tsohon ma yayi dariya yace "Toh muje..." Abuturrab ya kalli samantha ya kama hannunta suka bi bayansa, ya matsa hannunta a hankali yace "Dama kina jin fulfulde shine ko sau daya baki taba gaya min ba" ta d'an yi murmushi bata ce komai ba, haka suka dinga bin dattijon da shanayensa kusan ashirin, su sha wancan kwanan su fito ta wani su kuma shan wata kai hanyar dai gashi nan gashi nan, Abuturrab yasan ko kashe sa xa ayi kila baxae iya gane hanyar ba. Suna isa Rigar dattijon ya juya yana kallonsu da fulfulde yace "Ga 'yar rigar mu nan, da fatan xaku ji dadin xama a ciki na yau dai" murmushi kawai Abuturrab yayi, tafiyar minti goma suka yi suka iso wani gida dake xagaye da kara, Dattijon ya shiga hade da sallama suka bi bayansa, bukkoki hudu ne a xagaye a d'an karamin tsakar gidan, wata mata dake daka tsakar gidan tayi masa sannu da xuwa da yare tana kallonsu Abuturrab, ya amsa yace "Kin ganni da baki 'yan uwanmu koh?" Mikewa tayi ta dauko tabarma ta shimfida tana masu lale, Yace "debo masu nono kafin ki xauna Hansai" wani bukka ta shiga sae ga ta ta fito da kwarya cike da nono ta ajiye masu, Dattijon da ake kira da Alto yace "Ina yarinyar nan ta shiga?" Hansai tace "Taje kai fura gidan tuwaru nasan duk inda take ta kusa gida yanxu" Malam Alto yace "Toh akwae ruwa gidan koh? Allah ne yayi masu katanga da barayi suka afko daji shine fa muka hadu da su...." Girgixa kai Hansai ta dinga yi tana cewa "Allah yayi mana tsari" Wata yarinya da baxa wuce Samantha ba ta shigo gidan kanta dauke da icce, ta karaso ta durkusa ta sauke tace "Inna bak'i muka yi" Malam Alto yace "Ehh wllh gasu nan daga birni suke" ta kalli Samantha tace "Sannu da xuwa..." Hansai tace "Tashi ki shiga da ita ciki ki bata zani ta daura tayi wanka" Mikewa tayi samantha ta tashi ita ma suka shiga wani bukka, bbu komai ciki sae yar katifa da xani a kai, sae jakar gari yayi xafi guda biyu, cement din dakin duk ya farfashe, Samantha ta xauna kasa yarinyar da hausarta na fulani tace "Ki xauna kan katifa" samantha tayi yanda tace, yarinyar ta bude jaka ta fito da wani xanin kayan fulani a linke ta ajiye mata tace "Gashi ki daura" Samantha ta kalleta a hankali tace "ina son in huta ne" yarinyar tace "Toh ki huta" daga haka ta fita, Hansai tace "Kin bata xanin Binta?" Binta tace "Eh ta kwanta wai tana son ta huta" Hansai tace "Toh shknn, maxa ki xo ki hura wuta in daura sanwa tunda mun yi bak'i" Wani sabulu babba me kamshi Alto ya dauko a dakinsa ya mika ma Abuturrab yace "Aminina Hammadu ne da yaje birni ya kawo mun sabulun nn har uku... Gashi ka shiga wanka da shi xaka fi jin dadinsa" Abuturrab ya mike yana murmushi ya karba yace "Toh nagode Baffa" daga haka ya nufi 'yar kewayan dake tsakar gidan don Baffa ya kai masa ruwa Binta ta bi sa da kallo, ko da ya fito Baffa ya kai sa Bukkarsa ya dauko masa wani tsaftatattcen rigarsa irin ta fulani ya basa, Abuturrab ya karba hade da godiya Alto ya juya ya fita, yana gama shiryawa ya fada d'an gadon dake bukkar lkci daya bacci ya daukesa. Burabisko da miyar taushe da k'ashi Hansae tayi ta ajiye masu cikin langar tuwo da miya, Baffa dake xaune da yar radio a hannunsa yace "Bayin Allah da alama sun wahala, a dajin ma suka kwana" ana kiran Azahar Baffa ya tada Abuturrab yayi sllh, Hansae tace "Tafi ki tada ta ita ma tayi wanka tayi sllh" binta ta shiga ta tada Samantha tace "Ki tashi kiyi wanka sai kiyi sllh, Azahar yayi" Samantha ta mike xaune tana mitsika ido, can ta mike ta cire kayan jikinta ta daura xanin, ta kalli binta tace "ki ban mayafi don Allah" Binta ta nemo mata wani dankwali ta bata tace "Mu je in raka ki kewayen na kai maki ruwa" Abuturrab na xaune a tabarma tare da Alto yana shan fura da nonon da Hansai ta dama masu Samantha ta fito da Binta, kallonta ya dinga yi ita ko kallo daya tayi masa ta dauke kai Binta ta rakata har bayin snn ta dawo, Samantha na fitowa daga wankan Hansai tace "Ga buta can ki dauka kiyi alwala" shiru Samantha tayi bata ce komai ba, can ta kalli Abuturrab da idonsa ke kanta, ta girgixa kai a hankali tace "Bana yi" daga haka ta shige Bukkar Binta, wata yar top da xani binta ta bata ta sa, tana gama shiryawa binta tace "Ki fito ku ci abinci wae ke yake jira" Samantha ta mike suka fita a tare, Alto ya mike yace ta taho ta xauna, ta karasa ta xauna kan tabarmar, Fura Abuturrab ya mika mata ta karba ta ajiye, bata bari sun hada ido ba duk da irin kallon da yake mata, shi ya fara sa hannu cikin langar dake dauke da Burabisko da miya yayi bismilla ya fara ci, kasa sakewa Samantha tayi taki cin abincin sai fura da take sha a hankali Hansai tace "Ko xa ku shiga daga ciki naga kamar a takure take" Kamar Abuturrab jira yake yace "Toh" Hansai tace "Binta kai masu abincin daki" Binta ta je ta dau abincin ta shiga da shi bukkarta, Abuturrab ya mike yana kallon Samantha ita ma ta mike ta bi bayansa suka shiga Bukkar, suna shiga ya nuna mata kusa da shi ta xauna, ya dau cup din furan ya mika mata ta sa hannu ta karba yace "Finish it immediately ki ban cup din" ta yi d'an murmushi ta kai baki, kadan ta sha tace "Na koshi" ya hade rai yace "Sae fa kin shanye" girgixa kai tayi ya kwace cup din hannunta ya matso kusa da ita ya rike kan ta ya kai cup din bakinta, bbu yanda ta iya haka ta dinga sha kamar xata yi kuka, sae da ya ga ya wuce rabi snn ya ajiye ya ce "oya sa hannu" lekan abinci tayi tace "What's that" Hannu yasa ya deba ya kai bakinta, ta bude bakin a hankali ya xuba mata, da kyar ta dinga taunawa tana kallonsa kmr me taunar magani, ya dake bai bari yayi dariyar dake cin sa ba, tana hadiyewa tace "Baxan iya ci ba Dr " Ya girgixa kai yace "No, but da dadi fah, there's no other food than this!" Ta fashe da kuka tace "Baxan iya ci ba..." Shiru yayi yana kallonta, can ya kamo hannunta cike da tausayi yace "Toh me xa ki ci" cikin rawar murya tace "Rice!" *Haske writers asso*📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 30..... Shiru yayi ya rasa abinda xai ce mata, can ya sa hannu cikin aljihinsa yaga har lkcn kudin da yayi withdraw na nan, ya rufe burabiskon ya mike yace "To taso mu je" a hankali ta mike ta bi bayansa suka fita, yana kallon Hansai da Alto da yare yace "Baffa xa mu d'an xaga rigar nn...." Alto tace "Toh har kun cinye abincin ne?" Yace "A'a idan mun dawo xa mu ci, furan ya ishe mu" Alto tace "Toh bari Binta ta xaga da ku, sai dai fa ba wani girma ne da kauyan namu ba" tana dariya ta kare maganar shi ma yayi dariya yace "Ni kuma hakan ya burgeni sosai babu hayaniya" Alto ya kwalo ma Binta kira ta fito yace tayi masu jagora xa su xagaye Rigar garki, tace "Toh" snn ta koma ciki, dama shigar fulani tayi dogon gashinta da ke kai wa har kusan gadon bayanta an tufke mata shi gida uku, ta dau sandar kiwonsu tana kallonsu Abuturrab da fillanci tace "Mu je" Samantha dai ko kallonta bata yi ba har suka fita, tana tsakiyarsu suke tafiyar ko wani Bukka suka wuce sai ta fadi masu na wanene duk da fillanci, kai kawai Abuturrab ke kada mata, can ta kalli samantha da yaren tace "Ke bakya magana, ya sunan ki" Samantha bata ce komai ba, Abuturrab yace "Sunanta Fatima amma ana kiranta da Samha" kallonsa Samantha tayi ya wara mata ido, Binta tace "Lah ashe sunan mu daya, to me yasa kanwar taka bata magana?" Ya buda hannu yace "Haka take" tace "To kai ya sunanka?" Yace "Aliyu" ta xaro ido "Suna mai girma" Hira Binta ta dinga masa tun yana amsa mata da uhm da eh da A'a har dai ya fara magana, Samantha dai tafiyarta kawai take bata ko kallesu ba, Binta tace "Ina son wataran ni ma inje birni" kamar xata yi kuka ta kare maganar, yayi yar dariya yace "Kar ki damu xamu xo mu dauke ki wataran..." Tace "To a ina xan xauna ni da ban san kowa a birni ba" Yace "Gidanmu mana" tayi murmushi tace "Allah yasa kar ku mance da ni" yana murmushin shi ma yace "In'sha Allah" kallon Samantha yayi da fillanci yace "Are you okay?" Bata ce komai ba bata kuma kallesa ba, tsayawa yayi yana kallonta Binta ma ta tsaya, ita ko ta ci gaba da tafiyarta, ya jawota da damuwa yace "Samha tell me what's wrong?" Ta mayar masa da fillanci tace "Just want to be left alone" shiru yayi yana kallonta, ta kwace hannunta ta ci gaba da tafiya, Binta ta kallesa a hankali tace "Kilan so take ku je gun Ammin ku" Murmushi ya k'irkira bai ce komai ba suka ci gaba da tafiya, can ya kalli Binta yace "Akwai inda ake sai da abubuwan ci a Rigar nan" tace "Ehh mana akwae yar kasuwa, ana tsayar da warar fulani, hura da nono, gyada kai har da nama da...." Ya katse ta yace "Shinkafa fah?" Ta ce "Akwai mana" yace "Toh muje xan siya mata shinkafa xata ci" Binta ta kalli Samantha da tayi gaba can tana tafiya tace "Bata cin Burabisko?" Kai kawai ya gyada mata, ya karasa da sauri gun Samantha ya kamo hannunta da turanci yace "What's all this dear?" Bata ce komai ba, ya ci gaba yace "Did i offend you in anyway" Binta dake kallonsu ta gefen ido ta ci gaba da tafiya, ganin baxa ta kulasa ba ya ci gaba da tafiya yana rike da hannunta, shinkafar dari uku ya siya da wani miya da ke basa kyankyani, ita kanta Samantha da ganin yanda take kallon abincin kasan bbu yanda ta iya ne, suna gama siya yace su koma gida, wnn karan su biyu ya bari suka yi gaba yana biye da su a baya. Har suka isa gida bbu wanda yace komai cikinsu, Su Alto suka yi masu sannu da xuwa, ba laifi Samantha ta ci shinkafar sbda yunwar da take ji, ya tallabi cin dinsa yana kallonta har tace ta koshi, yayi murmushi yana gyada mata kai, murya can kasa yace "Kinsan me love?" Kallonsa tayi bata ce komai ba, a hankali yace "Idan ance ki tashi kiyi sllh ki dinga cewa toh" ta kafe sa da manyan idonta, can tace "Ban gane ba" ya lumshe ido ya bude cikin sanyin murya yace "I mean idan aka ce maki ga ruwan alwala ki ce to, ki dauka...." Wani kallo take masa tace "In yi me?" Yace "Kiyi alwalan ko baki iya ba!" Da mamaki ta dinga kallonsa, can ta girgixa kai tace "No!" Shiru yayi yana kallonta, can yace "Let me ask you, what's Good about Christianity?" Ta wani hade rai tace "What's Good about Islam?" Kamar jira yake yace "A lot, it's a religion of peace.... The true religion, Christianity is not a religion, it's just a way of life.... Ki bani inda aka ambaci Christianity a bible nima kuma xan baki inda aka ambaci Islam a bible...." Wani kallo ta dinga yi masa ya gigixa kai yace "If you know ur bible too well John 14;27 Jesus said 'Peace i leave with you, My peace i give to you, not as the world gives, and do not allow ur heart to trouble you' here Jesus made mentioned of the religion he practiced and let to his disciples (Followers) as (Shalom) and did you know the meaning of Shalom?" Har lkcn kallon tara saura qtr take masa, ya matso kusa da ita ya d'ago kanta yana kallon kwayar idonta yace "In kinsan Bible din ki sosai sanin ma'anar shalom baxai maki wahala ba... Ashe kawae ke 'yar muna Christian ce" kwace fuskarta tayi tace "Shalom means Peace!" Murmushin da ya baiyyana dimples dinsa yayi yana kallonta yace "Good, And that's the meaning of Islam (peace!), Jesus ya gargadi mabiyansa (disciples) kan cewar kada su bi son xuciya, kada su bi ra'ayinsu, but unfortunately they all followed their heart desire and got their selves the name Christianity, a name not found in the bible, a name gotten from Paul the apostle, paul shine yayi naming dinsa Christianity for his selfish interest domin a da ai ba masoyin Jesus bane Paul, true or false? Jesus acted like we muslims do, he fall with his face to the ground, but never dance, clap, or beat drum as an act of worship, did he?" Ya tambaya yana kallonta, ya girgixa kai yana murmushi yace "He never, let me add a prove to this, Matthew 26:29 read thus 'Going a little further, he fell with his face to the ground and prayed......" Murmushi yayi yace "you see, ba ace he clapped his hands, beat drum or danced ba, even till date the Coptic Christians still pray the way Jesus PBUH did, the jews in the holy land still pray the same way also!" mikewa tayi ta bar masa wajen ta koma kan katifar dakin tayi kwanciyarta hade da lumshe ido, murmushi yyi ya mike ya fice waje. Mami ce xaune parlor ta rafka uban tagumi, Hajiya Mariya ma na xaune gefen yayartata, sai Yakumbo dake tsaye kekam bakin nan uwa an taka teba a kan titi ta jefa ma Mami harara yayi sau ashirin a wajen, manyan 'ya yanta maza duk biyun na parlorn, sai Abba dake tsaye shima kamar dai the soldier he is, sojoji ne har biyu tsaye bakin kofa, ya juya ya kuma kallon Mami strictly yace "For the last time ki gaya min inda Aliyu yake...." buda baki tayi cike da bacin rai tace "Kai kana matsayin mahaifinsa baka san inda yake ba sae ni, ta ina xan san inda Aliyu ya tafi, haba a dinga adalci mana" a fusace yakumbo tace "Yo idan bai tambaye ki Aliyu ba uwar wa xae tambaya?? ba boyayyen abu bane kowa yasan bakin ku daya da d'an iskan, ni ko rantsuwa nayi baxan yi kaffara ba kinsan inda Aliyu yake...." Sae kuma ta fashe da kuka tace "Tur!! Mu dai duk xuri'ar mu daga farkonta har ixuwa yanxu bbu crista, ko tu6a66e, ban dai san a naku yanda abun yake ba...." Mariya tace "Mu ma haka, hasalima iyayen mu da kakannin mu duk malamai ne..." Yakumbo ta jefa mata wani matsiyacin kallo tace "keee kar ki min fitsara ban sako da ke ba daga tambaya?" Ko kallonta Mariya bata yi ba, Abba ya girgixa kai yana murmushin takaici yace "Hajarah duk abinda Aliyu ya xama kece sanadi, ke ce sila...". Mikewa Mami tayi tana murmushi tace "Sae yau ka sani kenan, ae tun da na nema masa karatu a Uk na biya, na kama masa gida mai tsada, na xuba masa abubuwan more rayuwa, naki sauraran shawarar kowa ni da 'yan uwana nace ae namiji ne shi ba mace ba, na rufe ido ban ji ban gani na hada masa kaya na kai sa Airport ya tafi can yayi rayuwarsa in a free way, bbu sa wa bbu hanawa shekaru d'aid'ai har takwas, What did you expect Col???" Daga haka ta nufi stairs Hajiya Mariya ta bi bayanta, kasa cewa komai Abba yayi ya bi ta da ido, yakumbo ta tafe hannu tana salati tace "Wato mu matar nan ke gaya ma magana koh?" *Haske writers asso*📚✍🏻 💫 *Noorul Huda*💫 By Khaleesat Haiydar 📚✍🏻 31..... Alhaji Umar ya saci kallon Abba da uwarsa bai dai ce komai ba haka d'an uwansa Alhaji Jibril, juyawa Abba yayi kamar xae tashi ya fice daga parlon, Alhaji jibril ya ce "Toh Allah ya kyauta, Allah ya kawo mafita yasa ya gane abinda yake shirin yi" Yakumbo ta fashe da wani kuka tace "Ae ni Allah ya isa tsakaninmu da Aliyu, wnn abun kunyar da me yayi kama da wani ido xa mu kalli 'yan adawan mu, me ya burgesa game da crista arniya, ni dai ina ganin jarabawa, Aliyu ya cucemu, yaro kamar shaidan, duk artabun da aka dinga yi jiya ace ba a kamasa ba har ya gudu ko ina ya tafi..." A bangaren mumy kuwa tun daga jiya har yau kuka ne ya xamto abincin ta da ruwanta, tayi kukan tayi xage xagen, tayi iface ifacen, banda bata hakuri bbu abinda yan uwa da abokan arxiki suke, har cewa tayi da ta sani tun daren shekaranjiya ta kashe samantha tasan ba ita a duniyar ne kawai da ace ta bi musulmi sun gudu, gidan nasu cike yake da members din Church dinsu, mata da maxa, pastors har daga kaduna da Abuja sae da suka xo, masu addu'a nayi, masu xirga xirga da Abban samantha xuwa gidansu Abuturrab nayi, da ace Dad din Abuturrab ba babban soldier bane da ya shiga uku don ba abu me kyau bane xae biyo bayan irin sintirin da suke fiye da su ashirin har da matasa, daga karshe tsawa yayi masu yace "Su je duk inda xa su su nemi Aliyu su kashe sa ya basu go ahead, kada wanda ya kara d'aga masa hankali tunda basa ganin kokarinsa, bbu yanda suka iya ga gida cike da sojoji, haka suka juya sumui sumui suka fita. Abuturrab na xaune tsakar gida suna labari hira da Abba bayan la'asar, Alto bata kuma cewa a ta da Samantha tayi sllh ba a tunaninta bata da tsarki ne, Binta na xaune tana sirfa gero sai dai duk motsin da idonta xae yi a kan Abuturrab yake sauka, yana lura da irin kallon da take masa, sae abun ya basa dariya ya dai ci gaba da hirarsa da Alto, Samantha ce ta fito ta nufi bandaki da sauri ta fara amai tun kan ta isa, mikewa Abuturrab yayi haka Alto da Hansae dake wanke wanke suka dings cewa subhanallahi, Abuturrab ya d'agota a rikice yace "Meya faru?" Ta fashe masa da kuka tana rike da cikinta tace "Ciwo yake min" Hansae ta kawo ruwa a buta tace "Ikon Allah to bara in jika ma sa6ara" Abuturrab ya karbi ruwan ya wanke mata fuskarta snn ta shiga da ita ciki. Kwanciya tayi ya xauna gefenta yace "It's ur period right?" Juyawa tayi bata ce komai ba, ya mike ya fita, Tsaye ya ga Hansai har ta jika maganin da tace, yayi murmushi yace "Ae baxa ta sha ba Baaba, bbu gun sayar da magani nan ne?" Alto yace "Kai da tafiya sosai, Binta ta raka ka gun da xaka samu babur ka hau, sae kayi kamar xaka shiga Gombe...." Abuturrab ya durkusa yace "ohh daga kauyen nan sae gombe?" Alto yace "A'a akwai kauyuka har uku a gaba..." Abuturrab ya mike yace "Toh shknn bari in je..." Tuni Binta ta dauraye hannunta tace "Mu tafi..." Ya kalleta yace "Ae na gane hanya yanxu, da kin yi xaman ki" Tace "Yo ae baka san inda xaka samu babur ba" Hansae tace "Gaskiya ne, bari ta rakaka gun sai ta juyo" toh kawai yace suka fita gidan, tun da suka fita Binta ke xuba bai kalleta ba bare ya tanka ta ba, tafiyarsa kawai yake, har suka isa inda babur uku suke sbda masu fita kauyen, duk machine din sun rube, Binta tace "Bako ne daga birni wae wajen kauyen nan xaku fitar da shi xae siya magani" Bata rufe baki ba ko wanne ya dinga cewa ya hau, na gabansa ya hau mutumin ya tada machine din, ya d'an kalleta yace "Sae na dawo" daga haka yace ma mai machine din su tafi. Sae kusan karfe shidda Abuturrab ya dawo rike da leda, Alto dake kade shanayensa a waje yace "Ka dawo?" Abuturrab yace "Ehh na dawo Baffa sannu da aiki" Alto yace "Ka dai samo maganin koh?" Kai Abuturrab ya gyada masa yace "Na samo" daga haka ya shiga, Binta kadae ce tsakar gida tana kwasan tuwo, ta washe baki tace "Har ka dawo Aliyu?" Kallonta yayi don sae da tasa Mami ta fado masa, ta fi kowa kiransa da Aliyu, yace "Na dawo! Bbu kowa dakin?" Tace "Ehh ita kadai ce" ya duka ya shiga Bukkar, xaune ya ganta ta hade kai da gwiwa, ya karasa a sanyaye ya ajiye ledan hannunsa ya d'agota yace "Samha!" Ta kallesa da idanuwanta da suka yi ja, cikin sanyin murya yace "Kuka kike?" Sauke idonta tayi ya kamo hannunta yace "Am making you suffer koh, i know you re not use to all this Samha.... But for the sake of my love endure it for just a while..." Ta fashe da kuka tace "Am not complaining" gefenta ya dawo ya xauna ya jawota jikinsa yace "Bance kina complain ba, but you re not use to this such of life..." Bata ce komai ba yace "Kin fara period din ne?" Ta girgixa masa kai, yace "But it's on it way koh?" Shiru tayi bata ce komai ba, ya dago kanta yace "Shareni ma kika yi" kwace kanta tayi tace "How did you know?" Yayi murmushi ya daura kansa a kafadanta yace "I know because i am a doctor...." Tayi masa wani kallo ta gefen ido tace "Ko dai sa ido, kawai don ka ga na yi amai?" Kamar xata yi kuka ta kare maganar, dariya yayi ya kai bakinsa kunnenta yace "Ni din, toh shknn in ma ya xo ya fara wahalar min da ke ko kallonku baxan yi ba, ya gama wujijjiga ki ya xuba abinsa ya wuce" murmushi tayi ta boye fuskarta a jikinsa, lkci daya Binta ta fado dakin, da sauri ya saketa ita ma ta ja baya, Binta na ganin haka ita ma da sauri ta fita, Ya kalli Samantha yaga ta wani hade rai, bai ce komai ba ya dau ledan da ya kawo ya bude, pad leda biyu sae inner wears da allurori da drugs, perfume, Toothpaste, brush soap da sponge sai gown har biyu da veil ya xube mata su gabanta, ta dauke kai bata ce komai ba, Ya bude daya ledan ya fiddo ledojin kaji biyu ya ajiye mata daya ya ajiye dayan a gefe, sae kuma Bread biyu da Blue band daya da ya siyo da kayan tea sae table water babba, mikewa yayi ya dau ledan kaza da daya bread din ya fita don kai ma su Binta. Bayan Isha Abuturrab na xaune tare da Baffa Binta ta fito tace "Aliyu ina jin fa ciwon cikin ne ya dawo sae juye juye take" Hansai dake cin tuwo tace "Subhanallahi, ka bata magungunan kuwa?" mikewa yayi ya shiga dakin Binta ta bi bayansa, ya durkusa gabanta yace "Sannu dear, but are you flowing?" Ta girgixa masa kai hawaye na sakko mata, dagota yayi ya bude ledan da magani ke ciki ya ballan mata biyu ya bata da ruwan goran ta sha, sae da yaga ta d'an nutsu snn ya mike ya fita, Hansai ce kadai a tsakar gida sai Binta da ta gaji da tsayuwa tun daxu dakin ta fito, Hansai tace "Ta samu bacci ne?" Yace "A'a ya mata sauki ne" Hansai tace "Toh Allah dai ya sauwake, dama ashe matar ka ce?" Kallon Binta yayi don yasan ta yi mata wata magana kenan, ya gyada kai kawai, tace "Allah sarki, ae ni nayi xaton kanwar ka ce, ashe mai daki ce, to shiga ciki sai ka tsaya tare da ita tunda ma bata da lafiya" yace "Toh" Hansai tace "Binta xata kawo maku bargo" juyawa yayi ya koma dakin, ba a dau lkci ba Binta tayi sallama bakin kofa ya fita ya karbi bargon ya dawo dakin, xaunawa yayi yana kallon samantha yaga har ta fara bacci, ya shimfida 'dan bargon a kasa ya rage lamp din dakin sosai ya kwanta. Can cikin dare ta kusa fadowa kansa bayan ta sauka daga kan katifa, ya mike xaune ya rikota yace "Me ya faru?" Rikesa tayi tace "Amai nake ji" ya rungumeta yace "Amma cikin ya daina?" Kai ta gyada masa, ya fara shafa mata bayanta a hankali murya can kasa yace "Aman xai koma kin ji?" Bata ce komai ba sae rufe idonta da tayi, haka ya dinga yi mata har taji aman ya koma, ta xame jikinta ta koma kan gado ta kwanta, ya jima xaune ganin kamar tayi bacci ya koma ya kwanta. Washegari da asuba tun da ya idar da sllhn asuba a dakin yayi ta tunanin inda xa su gashi bai da enough cash a hannunsa, kudin account din Hajiya Mariya ma bbu yawa, mikewa Samantha tayi xaune ya juya yana kallonta, ganin yanda ta bata fuska ya dawo kusa da ita yace "What?" Kamar xata yi kuka ta nuna masa cikinta, yace "Ya fara ne?" Ta gyada masa kai ta mike ta nufi inda ya ajiye kayan jiya ta dau pad da brush da toothpaste yana kallonta yace "In raka ki?" Wani kallo tayi masa yayi murmushi yana shafa kai yace "Ohk sorry" ko da ta dawo tilasta ta yayi ta ci bread da butter sbda alluran da xae mata, da kyar tana juye juye ta ci kadan ta sha ruwa yayi mata alluran ta kwanta, sae da gari ya fara wayewa snn ta samu bacci ya dauketa ya mike ya fita, Binta dake shara ta gaishesa da fillanci ya amsa yana tambayar ta tashi lfya, tayi murmushi ta tafi ta dauko wani flask da cooler ta dawo ta mika masa tace "Gashi karin kumallon ku" karba yayi yace "Mun gode" ya koma daki ya ajiye, tayi sallama bakin Hut din tace "Ga kofi" fitowa yayi ya karbi cup din ya koma ya ajiye, Muryan Alto ya ji da fillanci yana cewa "Ali na tafi kiwo sae na dawo" Abuturrab ya fito ya gaida sa, Alto yace "Ya mai jikin?" Abuturrab yace "Taji sauki Baffa, kilan baxa ka dawo ka same mu ba anjima xa mu dau hanya" Baffa yace "Allah mai girma, shi yasa ba a sabo da bako, baxa ku jira hat in dawo da rana ba" Abuturrab yayi murmushi yace "So nake mu isa gida da wuri ne" Baffa yace "Toh Allah ya tsare, ni bani da komai da xan baku, amma Binta xata tatsar maku nonon shanu ku tafi da shi bamu da komai baya ga wannan" Abuturrab yace "Ayya ba komai Baffa mun gode da karramawar ma" Alto yace "Toh Allah ya tsare, ku gaida mutan gida Allah ya tsare gaba" Abuturrab ya fiddo dubu goma cikin kudin jikinsa ya mika masa yace "Ga wannan ba yawa Baffa, in shaa Allah wataran xamu kawo maku ziyara" Alto ya bude ido yace "A yi haka?" Abuturrab yace "Kai dai ka karba Baffa" Alto ya karba da hannu biyu ya dinga sa masa albarka yana masu Allah ya tsare hanya har ya fita, Wanka Abuturrab ya shiga kewayen gidan yayi ya fito ya shiga Bukka, har lkcn bacci samantha take, ya shirya cikin kayansa da ya wanke jiya ya fita da na Baffa yana kallon Binta dake xaune tsakar gidan ita kadai yace "Baaba fa?" Bata kallesa ba tace "Ta je kauyen dake gaba da namu siyo gyero" yace "Ki ban sabulu xan wanke kayan nan" ta mike ta isa gabansa ta karba kayan tace "Xan wanke" yace "Noo, kar ki damu xan wanke" bata saurare sa ba ta nufi gun randar ruwansu ta diba, ya daga kafada ya juya ya koma daki ya bude flask din da ta basa ya ga kunu ne ya bude coolern ya ga kosai, diban kunun yayi ya dau kosan ya fita ya shimfida tabarma ya xauna ya shiga ci a nan, lkci lkci yake kallonta har ta gama wankin ta shanya kayan a igiyar dake tsakar gidan, ya koma inda take ta xauna, yace "Ke kin karya?" Gyada masa kai kawai tayi, yace "Yaushe Baaba xata dawo?" Tace "Kila tana hanya yanxu" yace "Bakya xuwa makaranta ne?" Ta kallesa tace "Yau alhamis" ya d'an buda ido yace "Haka fa" Bai kuma cewa komai ba, can tace "Bacci take ne?" Yace "Ehh" haka suka yi ta xama tsakar gidan shiru har Hansae ta dawo ya mike ya karbar mata kayan hannunta snn suka gaisa. Sai kusan tara da rabi Samantha ta tashi, har lkcn Abuturrab na xaune waje, ta mike ta dau sabulu da sponge ta fita, su biyu ne tsakar gidan shi da Binta dake wanke gyero, Samantha bata ko kallesu ba Abuturrab da ya bi ta da ido yace "Wanka xa ki yi?" Binta na jin haka ta mike tace "Bara in juye maki ruwan xafin ki" daga haka ta dau bokiti ta nufi gun murhu ta juye ruwan kai ta kai bokitin gun randa ta sirka ta kai kewaye tace "Bara in dauko maki sabulu" Samantha tace "Akwai sabulu a nn" Binta ta dauko kwando ta mika mata Samantha ta shiga bayin, mikewa Abuturrab yayi ya shiga daki. *Haske writers asso* Da fatan anyi sllh lfya Allah ya maimaita mana. 💫 *Noorul Huda*💫 By Khaleesat Haiydar📚✍🏻 32..... Samantha na shigowa bayan tayi wanka bata ko kalli Abuturrab ba ta nufi gun kayan da ya siya ta durkusa, can ta kallesa taga kallonta yake ta bata fuska tace "Kaya xan sa?" Ya wara ido yace "Na rike ki? Ki sa mana" tace "Toh ka fita" murmushi yayi yace "In fita gun Binta ki kuma daure min fuska" daukar abinda xata dauka tayi ta nufi kofa ya fixgota tace "Wayyo ni ka kyaleni kaya na xan je in sa a waje..." Ya wara ido yace "Toh me xa ki boye min da ban sani ba jikin ki!" Ta yi masa wani kallo tace "Ae dai na wasu ka sani ba nawa ba malam" Dariya yayi ya kai bakinsa kunnenta yace "See you, ke nakin ma special sani xan masa, sanin da bbu wanda xai kara masu har abada.... Only me" kwace kanta take son yi ya ki saketa, ta boye fuskarta jikinsa kamar xata yi kuka tace "Bana son irin haka Doctor" yana dariya yace "Toh na daina baby, but a nan xa ki sa kayan ki" bbu yanda ta iya haka ta shirya a dakin, and he pretend he's not looking at her, tana gama shiryawa ya xuba mata kunu ya mika mata ta sha kadan ta ajiye kosan ma bata ci ba, yana kallonta yace "Xa mu tafi yanxu!" Kallonsa tayi bata ce komai ba, can ta mike ta fara gyaran dakin, ya taimaka mata suka gama, sha daya suka fito xa su wuce, Hansai ta fito tana masu Allah ya tsare hanya tana cewa Allah sa ba shikenan an gama xumuncin ba, Abuturrab yayi dariya yace "In shaa Allah baxa mu mance ku ba Baaba wataran xa mu xo, dubu uku ya bata ta dinga godiya har da hawayenta, Abuturrab ya kalli Binta dake xaune nesa da su yace " Babu Sallama Fatima" kallonsu tayi yaga hawaye cike idonta, Hansai tace "Kaji shashanci to tashi ki rakasu mana" Samantha tayi ma Hansai sallama sannan ta fita, Ya karasa kusa da Binta ya durkusa yace "Nace maki xamu xo wataran fa..." Bata ce komai ba sae share hawayen idonta da take yace "Toh tashi ki raka mu" ba musu ta mike ta dau sandar ta na kiwo da nonon da ta tatsar masu yana gaba tana biye da shi a baya suka fita. Karasawa yayi ya kamo hannun Samantha yace "Baku yi sallama da Binta ba" ta kalli Binta ta gefen ido tace "Mun tafi Allah ya saka da alkhairi" kai kawai Binta ta gyada mata, daga haka yace "Mu je to ki raka mu inda xa mu samu Babur" gaba ta shiga suna biye da ita a baya, sun yi nisa sosai sai ga wata mota na tahowa a bayansu, Abuturrab yace "Wannan fa" Binta ta kalli Motar tace "Motar D'an lado ne, shi daya ne mai mota a rigar nan a birni yake aiki, da ka tsayar da shi ka ji inda xa shi ko?" Abuturrab ya tsayar da motar kamar yanda tace ae ko ya tsaya ya sauke glass, Abuturrab ya gaida sa mutumin da xai iya kaiwa arba'in ya amsa yana kallonsa, Abuturrab yace "Don Allah idan ba damuwa ina ka nufa?" Mutumin yace "Gombe xa ni...." Abuturrab ya d'an yi shiru, sae kuma yace "Toh mu ma can muka yi, xa a taimaka?" Mutumin yace "Ba matsala ku shigo" Abuturrab ya bude ma Samantha baya ta shiga ya rufe, ya kalli Binta da wasu hawayen suka cika idonta ya ciro dubu biyu duk da ya so bata fiye da haka ya damka mata a hannunta yace "Na maki alkawarin wataran xa mu dawo" da kyar ta yarda ya sa mata a hannunta ta mika masa nonon dake a leda ya karba yayi godiya sannan ya juya ya shiga front seat ya d'aga mata hannu ta juya da sauri ta bar wajen, D'an lado ya ja motarsa yace "Amma ba nn rigar kuke ba koh?" Abuturrab yace "Eh mu baki ne" D'an lado yace "Da alama kam, toh Allah ya sauke mu lafiya" daga haka ya maida hankalinsa kan tukin da yake da gani dae kasan hannunsa bai gama fadawa ba, ta madubi Abuturrab ya dinga kallon Samantha ganin yanda ta wani turo baki, dariya yake son yi amma ya dake, har suka isa gombe bayan tafiyar awa biyu da rabi bbu wanda yace komai cikinsu, Abuturrab sai kallon garin gombe yake yana tunanin to ina xa su, bbu wanda ya sani a gombe infact bai ma taba xuwa ba, D'an lado ya katse masa tunanin da yake yace "ina xa ku sauka kenan?" Abuturrab ya kallesa yace "Ko nan ne ka sauke mu" D'an lado yayi parking Abuturrab ya bude motar ya fita, ya xaga ya bude mata ita ma ta fito, ya karbi ledan kayan dake hannunta yayi ma D'an lado godiya ya ja motarsa ya wuce, kalle kallen wajen Abuturrab ya shiga yi, yana neman bankin da yake ajiya, yaga duka ukun a area din, yasan first bank da Gtb ba dai layi ba, hakan yasa yayi deciding ya shiga unity, ya kalle Samantha yace "xan shiga bank, sai ki jira ni waje or we go in 2geda" ta girgixa masa kai kawai tayi xamanta gaban bank din, shi kuma ya shiga ciki, direct ya tafi gun CC, bae wani jima ba aka xo kansa, yace yana son a duba masa ko nawa ne account dinsa, daga sama har kasa matar ke kallonsa, can tace "ATM din waje me yake yi, ko wayar ka fa?" Yace "Akwai layi sosai, waya kuma bani da, idan xa ki taimaka ki taimaka...." Da kamar xata yi magana sai kuma ta fasa, sai kuma tace "Fado account number" ya fada tayi danne dannenta snn ta kallesa ta kalli hotonsa dake jikin computer tace "Dubu dari shidda da ashirin" ya xauna yace "Good, na gode kwarai, ana sayar da withdrawal slip a nan?" Ta nuna masa gun da xai siya snn ta kira wani customer, yana xuwa ya dauka ya ciro dubu daya da aka ce ya bayar ya mika, ya ari pen ya cike slip din, dubu dari biyu ya saka yayi sign ya nufi gun Cashier, su ma sai da yayi masu jan ido wai wani yaje atm they re busy, yace "Haba wani atm xan je, ba fa dubu hamsin xan cire ba malam, kawai inje in bata ma masu cire dubu biyar lkci, awa nawa xan dauka ina cire dubu dari biyu? Plss answer me coz i wanna get out of here" Ba yanda suka iya haka suka karba bayan minutes din da basu wuce sha biyar ba suka basa kudin sa, nan ya roki alfarmar jaka aka basa ya xuba kudin yayi ficewarsa, ya isa gun Samantha yace "Am sorry Dear, tashi mu je" ta mike ya karbi ledan hannunta suka nufi titi, yana kallonta yace "Dear hotel fa xa mu je kafin mu samo solution" ta kallesa tace "Hotel?" Shiru yayi yana kallonta, ta dauke kanta, ya sauke ajiyar xuciya yace "Just for today dear.... Kinga bamu san kowa a gombe ba, it's my 1st time here" jin bata ce komai ba ya tsayar da mai adaidaita yace "Hotel mafi kusa xaka kai mu" sae da ya tsaya ta shiga sannan ya shiga, ba laifi hotel din na da kyau, ya biya kudin kwana daya dubu ashirin da biyar a reception aka basa makulli da room number, babban daki ne sosai da toilet a ciki, ya kalli samantha da har lkcn ta ki cewa komai ya xauna bakin gado bayan ya ajiye ledan hannunsa yana kallonta yace 'You followed me without trusting me kenan Samha..." Bata bari sun hada ido ba ta karaso dakin a sanyaye ta xauna can karshen gado, girgixa kai yayi ya mike ya bude jakar dake dauke da kudi ya cire dubu dari, ya sa a aljihu yace "Am coming back right away, me xa ki ci?" Cikin sanyin murya tace "Anything" ya juya ya fita ya kulle dakin, tagumi tayi tana tunanin anya did she made the right decision following him and neglecting her dear parent, hawaye ya cika idonta ta fada kan gadon ta fashe da kuka, Why is all this happening to her within just 2 months, she know God will never forgive her for doing this to her parent, but she love him and they will never allow her to be with him, tayi kukanta me isarta ta mike ta dau soap da sponge, toothpaste da sponge ta shiga bayi dake dakin, wanka tayi ta fito ta shirya tayi kwanciyarta nan da nan bacci ya dauketa, bayan azahar Abuturrab ya dawo, ya ajiye ledan hannunsa yana kallonta, bai tada ta ba ya shiga toilet ya dauro alwala ya xo ya gabatar da sllhn Zuhur, ya jima xaune yana addu'a daga bisanni ya mike ya shiga bayi yayi wanka ya fito ya shirya cikin daya daga cikin kananun kayan da ya siyo, ya bude fried rice din da ya siyo masu da drinks ya ci wanda xae ci ya ajiye sauran, kwalin karamar waya ya dauka ya bude ya ciro wayar ya sa sabon sim din da ya siyo ya kunna wayar, ya loda airtime yayi dialing number Hajiya Mariya gabansa na faduwa a xuciyarsa kuwa addu'a yake Allah yasa ita kadai ce a gun, bugu daya biyu ta d'aga, ya shafa kai a hankali yace "Mumy!" Hajiya Mariya dake xaune daki tare da Mami da frnds dinta biyu, ta saci kallon Mumy ganin kallonta take tace "Helloo!" Abuturrab yace "Ina ji Mumy ina yini...." Hello... Hello... Abinda ta dinga cewa kenan can tayi tsaki ta katse, Hajiya Maimuna tace "Network koh?" Hajiya Mariya tace "Ae kuwa...." Hajiya salaha tace "Toh da ki fita waje...." Hajiya Mariya ta tabe baki tace "Kila kiga ya dawo kuma" Abuturrab da sharp thinking yana jin reaction dinta yasan ba ita kadai bace a gun don haka bae sake kira ba, Mikewa Hajiya Mariya tayi tace "Bari dai ban san ko masu bani kudi bne bari inje waje" daga haka ta fita, bata ko kalli Abba dake parlor da abokansa ba tayi ficewarta waje, Abba ya bi ta da kallo, can ya girgixa kai yace "Wannan Mariyar ma ban yrda da ita ba bakinsu daya da Aliyu, ba abun mamaki bne ma tasan inda yake!" Col Usman na girgixa kai yace "ban taba ganin mai taurin kai da tsaurin ido irin Aliyu ba...." Abba yace "Duk ya kuskura ya shigo hannuna wllh sae bullet ya kare a kafafuwansa..." Har kofar gida Hajiya Mariya ta fita sanin halin mijin yayarta, tana fita ta kira number da sauri, Aliyu naganin kiranta ya daga, tace "Aliyu!!" Ya buda ido yace "Mumy..." Tace "Kuna ina Aliyu?" Shiru yayi, tace "Ohh ni din ce yanxu kuma baxa ka gaya ma inda kake ba" yace "Ke kina ina Mumy" ta hade rai tace "Ina tambayarka kana tambayata..." Ya sauke ajiyar xuciya yace "Kiyi hakuri Mumy, but don't say anything to anybody plss...." A fusace tace "Uwarka! ni kake gaya ma haka da can ban ce komai ba sae yanxu" bae san lkcn da yayi dariya ba yace "Yi hakuri Mumy, ina Gombe!" Ta xaro ido tace "Gombe kuma Abuu, wa ka sani a can?" Ya girgixa kai yace "Ba kowa wlh..." Da damuwa tace "Yarinyar fa?" Ya kalli Samantha dake ta bacci yace "Ga ta Mumy, she's sleeping" Hajiya Mariya tace "Kaji tsoron Allah Aliyu, kada kayi using wnn advantage din a kan baiwar Allah don tana sonka, kar ka manta ba fa matar ka bace, don't use her....." A sanyaye yace "Mumy baki yadda da Aliyun ki bane kuma, kema kin san ba hali na bane" Hajiya Mariya tace "No son! Kasan sha'anin rayuwa, bbu abinda shaidan baxae iya yi ba...." Sosai jikinsa yayi sanyi yace "In'sha Allah Mumy xan kiyaye.... Mami fa?" *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 33.... Hajiya Mariya tace "She's inside" ya d'an yi shiru sai kuma yace "Abba fa" tace "Yana nan.... But you re in trouble in har ka shigo hannunsa" Aliyu yayi murmushi yace "Na sani" da damuwa tace "Ka dai kula Aliyu tausayin yarinyar nake, tunda har ta guji iyayenta sbda kai, jan ra'ayinta xuwa musulunci baxai yi wahala ba" Yace "Hakane Mum, dama am planing of marrying her soon don ban son in cuceta, i don't want her to regret trusting me, idan nayi haka komai xae fi zuwa da sauki" Hajiya Mariya tace "Anya, naga kamar ya fi ka jira sae ta amshi musulunci, kar ta ga kamar kana using advantage din auren ne..." Bude gate ta ji anyi da sauri tace "Za mu yi waya Aliyu, don't call again xan dinga kiran ka..." Daga haka ta katse wayar, Abba ta gani bakin gate waya kare a kunnensa ya rako abokansa xa su wuce, tayi dialing din number wata da xata bata kudi suka yi magana snn ta juya ta nufi gate din ya bata hanya tayi wucewarta, bin ta yayi da kallo har ta shiga cikin gida, ya juya ya koma ciki shi ma bayan abokan sun shiga mota, ya shiga part dinsa ya kira Mami, bbu bata lkci Mami ta iso, yana tsaye bakin window rungume da hannunsa (Inda Aliyu ya gado rungume hannu knn, lol" ya juyo yana kallonta yace "Hajarah! i won't take it likely with ur sister idan naga da sa hannunta a abubuwan nan da Aliyu yake, xan ajiye cewar yar uwarki ce a hukuntata yanda ya kamata...." Mami tace "Ban yi mamaki ba... You can do more than that, yanxu kuma ka bar xargina ka koma xargin yar uwata" ya daga kafada yace "Ni dae na gaya maki" juyawa tayi ta fice daga dakin, dakin su Ramla ta shiga ta ci kukanta Ramla na lallashinta kafin ta fita ta koma dakinta, Hajiya Mariya na ganin Abba ya kira Mami dama ta yi saving din number Aliyu da wani suna daban tayi deleting dinsa daga call log, ko da Mami ta shigo dakin Hajiya Mariya na bathroom, ta dau wayarta ta fita, kiranta na karshe ta kura ma number ido, can tayi dialing taji muryar mace, ta dudduba dai bata ga alamar komai ba ta koma daki, Hajiya Mariya bata tambayeta dalilin daukan wayarta ba sae harkan gabanta take. Tunani Abuturrab ya dinga yi ko dai gida xae kama masu nan gombe ne, duk ya rasa takamaiman solution, kallonta yayi ganin tana juye juye kan gado, can ta mike xaune yace "Cikin ya fara koh?" Ta gyada masa kai, ya mike ya dauko mata abinci yace "Sauko ki ci in maki allura" ba musu ta sauko ya bude mata abincin ta fara ci, alluran ya hada ya ajiye yana jiran ta gama, bata wani ci da yawa ba ta mike yace "Sauran fa" da kyar tace "Anjima xan ci" daga haka ta kwanta ya mike ya karasa kusa da ita yayi mata alluran, Finger dinta ya kura ma ido ganin har lkcn xoben da ya sa mata na nan, ya kama hannunta a hankali yace "Samha!" Dago kai tayi ta kallesa, ya sakar mata murmushi ya kai lips dinsa kan hannun cikin sanyin murya yace "I will never let you down dear, i will be ur hero, i will be ur everything...." Hawaye ya cika idonta ya dago ta ya rungumeta, ta fara kuka a hankali, jin tayi shiru ya dago kanta a hankali ya ga idonta a lumshe, kwantar da ita yayi ya mike ya nufi window yana tunanin next action din da xae dauka, can ya dau kudi ya fita, wani me taxi ya tsayar bayan tsayuwar kusan minti sha biyar a bakin titi duk yana duba responsible cab man da xae tsayar su yi magana, yana kallon mutumin yace "Pls ina d'an tambaya ne" cab man din yace "Allah yasa na sani" Abuturrab na shafa beard dinsa yace "Kasan inda xan samu agent... I mean their office, anywhere around?" Mutumin yace "Wae na gida?" Abuturrab yace "Yes!" Mutumin yace "Wanda na sani da nisa daga nan, sae dai..." Abuturrab yace "No mu je kawai ka kai ni" daga haka ya shiga mutumin ya ja taxi din. Tafiyar kusan minti ashirin suka yi suka iso office din wasu agent, Abuturrab ya fito yayi masa godiya ya basa dari biyar ya shiga office din, ba shi ya fito ba sae kusan karfe shidda bayan an basa tabbacin nan da xuwa gobe xa a karbar masa gida. Ko da ya dawo lodge dinsu tana bathroom tana wanka, ba a dau lkci ba ta fito daure da towel, tana ganinsa ta tsaya nan bakin kofa, yace "Naga alamar ba kya gajiya da wanka yarinyar nan...." Murmushi tayi bata ce komai ba ya mike xae shiga yayi alwala ta durkusa da sauri tace "Nooo" xaro ido yayi yace "Ina ruwana da ke?" Murmushi yayi ya shiga toilet din, ta mike da sauri. Ko kafin ya fito har ta gama shiryawa, yana kallonta yace "Xan je mosque, will be right back" ta gyada masa kai ya fita, sae bayan Magrib ya dawo dakin, ya ganta xaune shiru da alamar tunani take, ya karasa kusa da ita ya durkusa ya ajiye ledan fruits din hannunsa yace "Sorry Dear, na jira anyi magrib ne" ta d'an yi murmushi bata ce komai ba, ya xauna ya bude mata ledan fruits din yana kallonta, Apple ta dauka ta kai baki a hankali, shi ma ya dauka ya kai daya baki, wayarsa dake kan gado ya fara ring, ya dauka yana kallon screen din yaga Hajiya Mariya ce, ya daga ya kai kunne yace "Hello Mum!" Tace "Aliyu where is she?" Kallon Samantha yayi ya mika mata wayar yace "My mum!" Ta sa hannu ta karba ta kai kunne, Hajiya Mariya tace "Ya kk Samha?" Samantha tace "Lafiya Mumy ina yini?" tace "Lafiya lau, kiyi hakuri kin ji, Allah na tare da ku, kar ki sama kanki damuwa...." Kai kawae Samantha ke gyada mata kamar tana ganinta. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 34..... Mikewa tayi a hankali ba tare da ta kallesa ba ta dau rigar baccin ta shiga bathroom, ba a dau lkci ba ta fito, kallo daya yyi mata ya dauke kai, ta nufi kan gado a hankali ta kwanta ta juya masa baya, bayan kusan minti goma ya mike ya cire shirt din jikinsa ya shiga bayi, ko da ya fito kashe tvn dake aiki yyi ya kashe wutan dakin ya karasa gado ya kwanta, a hankali ya birgina inda take, cikin sanyin murya tace "Doctor..." Yace "Samha...." Bata ce komai ba ya juyo da ita ya kwantar da ita kan faffadan kirjinsa yace "Sleep tight love, am with you" ta lumshe ido tayi lamo jikinsa, a haka har bacci ya dauketa, a hankali ya kwantar da ita ya mike ya koma kujerar dake dakin yayi kwanciyarsa amma ya kasa bacci sae juye juye yake, can dae ya mike ya shiga bayi ya dauro alwala ya fito ya tada sllh, sae kusan karfe uku da rabi ya samu yayi bacci, da asuba a masallacin dake cikin Hotel din ya fita yyi sllh sae da gari ya waye ya shigo masu dakin da breakfast, har ta shirya ya sameta, yana kallonta da mamaki yace "Ina fita kika tashi amma koh?" Kai kawai ta gyada masa, yayi murmushi yace "Alryt xo kiyi break kafin in shirya" daga haka ya shiga bathroom, ko da ya fito har ta gama cin abinda xata ci, yace "Are you sure kin koshi?" Ta gyada masa kai, shiryawa yayi ya ci chip da egg din kadan ya mike yace "Bacci nake ji Samha, let me sleep small" murmushi tayi ta mike xata gyara masa gadon yace "Noo don't worry dear...." Daga haka yayi kwanciyarsa, ta koma ta xauna ta rufe sauran breakfast din, yana kwanciya bacci ya daukesa, ita dai tana xaune idonta a kan tv, sae dae ko kadan ba sanin kan film din da ake tayi ba, tayi nisa a tunanin da take, Abbanta kawai take tunani wanda hakan yasa hawaye ya cika idonta, why did she accept to leave her family because of Aliyu, hade kanta da kujera tayi hawaye na sakko mata sae a snn take jin bata kyauta ba, tayi kukanta mai isarta daga nan ita ma bacci ya dauketa don yanda bai yi wani bacci ba haka ita ma bata jiya ba daren jiya duk tana kallonsa yana sllh, sai kusan goma da wani abu Abuturrab ya tashi, ganin yanda ta kife kai ya mike da sauri ya isa gabanta ya dafa ta yace "Samha" dagowa tayi da sauri tana kallonsa, kallon idonta ya dinga yi, da damuwa yace "Kuka kika yi?" Ta sunkuyar da kanta ya dago ta yace "Samha you re regretting everything koh?" Ta fashe da kuka tana girgixa masa kai, duk ya rikice yace "No plss samha, kar ki min kuka don Allah, naji xan maida ki gida...." Da sauri ta girgixa kai cikin sanyin murya tace "Am not regretting" yace "Toh me yasa kike kuka" goge hawayenta ta shiga yi cikin sanyin murya tace "Its just.... We re in trouble" ya lumshe ido ya kamo hannunta yace "Allah na tare da mu Samha, kar ki damu kin ji" sunkuyar da kanta tayi, yace "Tashi ki raka ni!" Ba musu ta mike ya kashe kayan kallon yace "Mu je" kofa ta nufa ya bi bayanta, suka fita ya kulle dakin, gun agents din jiya ya tafi, suna isa daya daga agent din yace su je ya ga gidan ko yayi masa, a motar agent din suka tafi, gida ne babba hadadde mai flats biyu, gidan na dauke da dakuna uku manya, Abuturrab ya kalli Samha yace "You like it?" Sunkuyar da kai tayi, yayi murmushi yace "Alryt, yallabai gidan yayi, thanks much" bbu bata lkci Abuturrab ya biya komai na gidan kusan 450k, da yamma bayan sun dawo hotel din yace "Xuwa jibi sae mu koma can koh dear?" Kallonsa tayi bata ce komai ba, ya kamo hannunta yace "Kin yi shiru?" Murmushi tayi bata ce komai ba. Washegari Abuturrab shi kadae ya fita ya bar ta tana bacci don xuwa can gidan ya ga abubuwan da ya kamata ya xuba, a ranan yayi furnishing gidan gaba daya, har food stuffs sae da ya siya, ya kashe kudi ba na wasa ba, da yamma ya koma hotel, Wanka ya sameta tana yi, yyi kwanciyarsa don ya gaji, washegari da ya kasance alhamis misalin sha daya suka tafi can gidan, nan ya fara tunanin anya xae yi ynda Hajiya Mariya tace masa kuwa, bai jin xae iya xama gida daya da ita bayan ba muharramar sa bace, idan shaidan bai ci galaba kansa yanxu ba yasan ko a jima ko a dade akwai ranan da abinda yake gudu xae iya faruwa, don yanxun ma he's just fighting his self from inside, kwanciyarsa yyi a parlor yana tunanin next step din da xae dauka, ana kiran Azahar ya mike ya shiga toilet dake nn parlor ya daura alwala ya fita xuwa masallaci, ko da ya dawo a kitchen ya sameta ta daura girki, ya rungume hannayensa yana kallonta yace "Weldone dear..." Murmushi kawae tayi ta ci gaba da wanke shinkafar da take yi, ya juya ya fita xuwa balcony yayi xamansa, wata dattijuwa da baxata wuce 50 ba ce ta fito daga daya flat din idonta sanye da medicated ta rike jaka ta nufi parking space dake part din nasa ta bude daya daga motocin dake wajen ta shiga ta tada, horn tayi bayan ta fito compound din, Abuturrab ya kuma kallon motar ya dauke kai don yasan lkcn da yake dawowa daga masallaci lkcn mai gadin ya tafi, tayi horn yayi sau uku, can Abuturrab ya mike ya isa gate din ya bude mata, sauke glass tayi ta karasa gate din da motar tana kallonsa murmushi dauke fuskarta tace "Nagode kwarai..." Ya dukar da kai yace "Ina yini?" Tace "Lafiya lau, kai ne new tenant din Apartment din can kenan?" Kai ya gyada mata yace "Nine..." Tace "Maa sha Allah, you re welcome, tare da mai dakin ka koh?" Ya d'an yi jim sai kuma da sauri yace "Ehhh" tace "To sannun ku da xuwa, ni ce occupant din flat din can with my 3 kidz... Hope xa mu dinga ba makwabtaka hakkin sa" murmushi yayi sosai yace "In shaa Allah" ita ma tayi murmushin tace "Maa sha Allah, it's nyc meeting you, na fita aiki sae na dawo" yace "Toh Allah ya tsare" daga haka ta ja motarta ta fita ya rufe gate din, haka kawai yaji matar ta burgesa sae yake ganinta kamar Maminsa, yana murmushi ya koma balcony yayi xaman sa. Shinkafa da miya Samha ta girka tana gamawa ta fito ta gansa har lkcn yana balcony, ta jingina jikin kofa tace "Na gama" ya kalleta ya wara ido yace "Weldone sweetheart" murmushi tayi ta juya ta koma ciki ya mike ya bi bayanta, a tare yasa ta xuba masu abincin don yana son ta ci da yawa, ai ko haka yayi ta forcing dinta har suka cinye abincin, ya tagumi yace "But wa ya koya mamaki girki haka dear?" Tace "Uhm My mum" ya lumshe ido yace "You are a very good cook" a hankali tace "Thank you..." Yace "No thanks baby, bari in je masallaci it almost time for salat" tace "Toh" ya mike ya shiga toilet ya daura alwala ya fita, ta kwashe plates din don xuwa kitchen ta wanke.Bayan magrib yana dawowa daga masallaci matar daxu na shigowa, tsayawa yyi har tayi parking ta fito kafin tace komai ya gaisheta, da fara'a ta amsa tace "Mai dakin naka na ciki in shiga mu gaisa mu san juna..." Yace "Da ki bari xamu shigo yanxu tun da daga aiki kike ai" tace "Toh shknn ina jira" daga haka ta nufi bangarenta. Abuturrab ya juya ya shiga cikin gida, bedroom ya sameta yace "Samha, taso mu gaisa da new neighbor dinmu" ta kallesa tace "Do we need to?" Yace "Yess dear!" Mikewa tayi yace "Ki sa Hijab..." Ba musu ta dau daya daga sabbin Hijabs din da ya siya mata ta saka snn suka fita yana gaba tana biye da shi a baya, kararrawa ya danna ba a dau lkci ba wata yarinya da baxata wuce Samantha ba ta bude kofar, kallonsu ta shiga yi, Abuturrab yace "Hello, mum dinku na ciki koh?" Ta basu hanya tace "Ehh, welcome" Abuturrab ya shiga parlon Samha ta bi bayansa, sosai parlon ya hadu da gani dai kasan Naira ta xauna, xama yayi kan kujera ya nuna ma Samha gefensa ta xauna, yarinyar ta wuce ciki sae ga ta tafito tare da Mum din tasu, da fara'arta ta karaso parlon tana kallon Samha tace "Sannunku da xuwa" Samha ta sauke kai kasa ta gaisheta, ta amsa mata da murmushi tace "It's nyc meeting you... Ya sunan ki?" Satan kallonsa Samha tayi, yana murmushi yace "Samha!" matar tayi murmushi ita ma tace "toh kai fa?" Yana shafa kai yace "Aliyu...." Ta buda ido tace "Maa sha Allah ashe Abbana ne, amma sabon aure kuka yi koh?" Yar dariya yayi yace "Ehh haka ne" tace "Ae naga alama, Allah ya kawo Zuri'a dayyaba, ni sunana Hajarah...." Wara ido yayi yace "Mum dita knn..." Tace "Kai haba, shknn na samu d'a kuma babana..." Yayi dariya tace "Allah kuwa, muna xaune da kidz dina uku a nan, babban son dina Muhd na Uk, sai kanwarsa Maryam da ke Cairo tana aure, snn Fatima da Khadija da autata Rabi'ah, Ba mu yi shekara a garin Gombe ba don da a Abuja muke, yanxu haka ma Mai gidan na can sae dai yaxo week ends, am running my late dad's clinic dake nan ne shi yasa...." Abuturrab ya kalleta yana murmushi yace "Maa sha Allah Mami, Allah yayi jagora" tace "Ameen, amma a gombe ku ke?" Ya girgixa kai yace "A'a kano muke..." Tace "Ikon Allah, toh Allah dai ya bada zaman lafiya, kaga bata da kowa nn dont make her feel lonely ka dinga kyautata mata a ko da yaushe Abbana" yace "In shaa Allah Mami nagode" Hajiya Hajarah ta kalli Fatima dake xaune tana dannan waya tace "Ko ruwa baxa ki kawo masu ba Teemah" Abuturrab yace "Noo Mami Alhmdllh, xamu koma ne ynxu" Hajiya Hajarah tace "Toh shknn Boy, na gode kwarai" yar dariya yyi ya mike ya kuma yi mata sallama haka ma Samha snn suka fita. Sae da suka koma part dinsu yana kallonta yace "You like her?" Murmushi tayi ta xauna bata ce komai ba, da damuwa yace "Why ba kya son magana Samha, you re just nt ur self" ta wara ido tace "Ba komai fa, is just change of environment" yace "U will like it soon dear, nt when am with you" murmushin dae tayi, ya gyada mata kai snn ya shiga daki. A parlor yyi isha sbda hadarin da ya hadu ga iska ana yi, ita dai tana xaune parlon sae kallonsa take har ya idar, yana kallonta murmushi dauke fuskarsa yace "Ko kema kina son ki iya sllhn ne?" Tace "Uhmm" yace "Yeah dear sae in koya maki it's nothing ae" yar dariya tayi yayi shiru yana kallon fararen hakoranta tace "Wa yace maka ban iya ba?" Yace "A ina kika iya?" Tace "Uhm, na xauna gun kanwar Abbana Anty Aisha a kaduna, during my jss can nake xuwa yin long holiday, idan su Mumy xa su Jerusalem can ake kai ni, tare take hada ni da yaranta mu je islamiyya, in dai xa ayi sllh nima sae nayi a gidan, har na xo na saba idan na dawo gida sai in ta yin irin abubuwan islam shknn Mumy ta hana Abba ya kai ni kaduna kuma, at that time ina jss3, har yau kuma ban sake xuwa ba" Abuturrab dake ta kallonta ko kiftawa bbu yace "Yanxu kin iya alwala knn?" Tace "Uhm har da sllh ma, kasan suran da muke lkcn a islamiyyar da muke xuwa?" Da sauri yace "A'a" tace "Mulk" ya lumshe ido yace "Kuma kin iya?" Dariya tayi tace "May be xan iya yi da qur'an because i know the arabic letters very well" kallonta kawai yake can yyi murmushi yace "Gobe xa ki min in ji" mikewa tayi tace "Xan yi bacci...." Yace "Ohk dear ki rufe windows sbda ruwa" kai ta gyada masa ta nufi daki tana adduar Allah yasa kar ayi ruwan sbda tsoron tsawa da take. Washegari da safe wajajen karfe tara tana daki tana bacci Abuturrab kuma na xaune parlor sae missing system dinsa yake ga parlorn bai sa kayan kallo ba tukun, yasan accnt dinsa ya d'an girgixa da cire ciren kudin da yake in kuma xa aci gaba da haka to fa karewa xa suyi, ga credentials can gida bare ya fara neman wani aiki, Tausayin Maminsa kawae yake amma in dan Abbansa ne ko a jikinsa don dama sun saba irin haka, Ring din bell aka yi, ya mike yana kallon kofar, can ya karasa ya bude, daya daga yarinyar Hajiya Hajarah ce tsaye bakin kofar rike da basket me dauke da breakfast, ya d'an koma baya, tace "Mum tace a kawo" yace "Ohkk thanks soo much" daga haka ya karba ta juya ta wuce, ya koma parlor ya ajiye, ji yyi matar ta burgesa sosai sae yake jin ta a ransa kamar Mami, bude abincin yyi yaga wainar shinkafa ce ta miya sae brown yam and egg da fries egg with plantains, a wani karamar warmer kuma ga Irish, murmushi yayi ya koma yyi kwanciyarsa kan kujera, sae kusan karfe goma Samha ta fito cikin shirin doguwar riga amma ba abaya ba, karasowa tayi parlon ta xauna kasa ta sunkuyar da kai ganin yanda yake kallonta cikin sanyin murya tace "Ina kwana" ya mike xaune yace "Lafiya lau dear, ashe kin iya bacci kema haka" murmushi tayi bata ce komai ba, ya nuna mata breakfast yace "Gashi Mami tace a kawo mana" ta kalli abincin a hankali tace "Mun gode" ya mike tsaye yace "Dama ke nake jira, let eat" ba musu ta mike suka isa gun breakfast din. Da rana mai aiki ne ta kawo masu lunch, Abuturrab ya karba yana kallonta yace "Hajiya na nan ne?" Ta girgixa kai tace "Ta fita aiki tun safe" yace "Alryt" Da yamma bayan la'asar yana zaune bakin gate tare da mai gadin gidan Hajiya Hajarah ta dawo, gaisheta yayi ta amsa da murmushi tace "Ya gidan?" Yace "Alhmdllh Mami ya aiki?" Tace "Alhmdllh, ina Samha?" Yace "Tana ciki" tace "Toh a gaisheta" yace "Mami mun gode for the food" tace "Ohh it's nothing Boy" daga haka ta ja motar ta ta shiga gidan. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 35.... Yau kwana goma sha hudu da xuwan su Gombe, yana xaune parlor laptop a gabansa sae dai gaba daya hankalinsa baya kan abinda yake, damuwarsa daya yanda yake cire kudi a account gashi ba shigowa wasu ke yi ba, at all shi bai iya sana'a ba bae ma san yanda ake yi ba, he don't want to run short of money, ya lumshe ido ya rike kai yana tunanin mafita, dago kai yayi bayan kusan minti goma jin fitowar Samha daga kitchen, kallonta yake har ta karaso parlor ta xauna, ya sakar mata murmushi yace "Weldone" jin bata ce komai ba yace "Dear!" Ta kallesa ya ce "An fara Reg din Jamb, gobe sae mu je ki yi koh?" Kallonsa kawai take bata ce komai ba, yace "Yeah gobe da safe in shaa Allah" daga haka ya mike ya shiga daki. Suna breakfast the next day ya sa ta shirya suka fita reg din Jamb din, sae kusan da rana suka dawo gida, bae bari tayi girki ba ya fita ya siyo masu abinci, daren ranan ya dinga tunanin ko dae ya kira small mum dinsa yyi mata maganar CV dinsa ne, yanke shawarar yin hakan yayi daga karshe, washegari lahadi yana xaune balcony ya hango Hajiya Hajarah xaune daga nata Balconyn da laptop gabanta, ganin ta kallo inda yake ya mike ya nufi gun ta, ya d'an dukar da kai yace "Ina kwana Mami?" Tana murmushi tace "Lafiya lau Boy, ya gidan?" Yace "Alhmdllh..." Tace "Ina Samha?" Yace "Tana ciki Mami" tace "Alryt wai in tambaye ka boy..." Kallonta yayi da sauri yace "Ina ji Mami" ta ajiye pen din hannunta ta nuna masa kujerar gabanta tace "To xauna" Ba musu ya xauna tace "Transfer aka yi maka xuwa garin nan?" Ya sunkuyar da kai yace "A'a Mami" tace "Ohk, naga kuma har yanxu baka koma aikin ba ko hutun mai yawa ka dauka, or rather let me put it this way...." Shiru ya d'an yi sai kuma yyi murmushi yace "Mami bana aiki yanzu" da mamaki tace "Baka aiki kuma?" Shiru yayi nan ma, ta sauke ajiyar xuciya tace "It's ohk Boy kar in shiga rayuwar ka koh!" Yar dariya yayi yace "Noo Mami ba haka ba, laifi nayi ma Abbana ya amshe CV dina and everything, that was why i left kano" kallon mamaki take masa, can ta girgixa kai tace "Duk a dalilin auren da kayi knn?" Ya gyada mata kai yana murmushi, tace "Toh ba a son yarinyar ne a gidan ku" nan ma ya gyada mata kai, tayi shiru tana kallonsa, sosai ta ji tausayinsa, can tace "But me yasa ka xabi aurenta da kayi ma iyayenka biyayya" A hankali yace "Mami haka Allah ya so" tace "Toh iyayenta fa?" Yace "Su ba ruwansu" Tace "Satin ku nawa da auren yau?" Yyi shiru kamar mai nazari sai kuma yace "Sati biyu da kwanaki" girgixa kai tayi tana kallonsa tace "Ur field?" Dago kai yayi ya kalleta yayi d'an murmushi yace "Am a Medical Doctor" kallonsa kawai take kafin tace "A doctor?" Yace "Yes Ma'am" ta cire glass din idonta tace "Where did you schl?" Yace "Uk nayi karatu Mami!" Tace "Ina matakin karatun naka?" Yace "Nayi degree, snn nayi masters duk a fannin medicine..." takardar dake gabanta ta dauka da pen ta mika masa tace "Am ur patient suffering from Malaria Typhoid, prescribe me drugs and injections...." Yar dariya yayi ya karbi takardar yace "Alryt Ma'am" ya gama rubuce rubucensa bayan kusan minti shidda sannan ya mika mata takardar ta karba ta sa glass dinta tana kallo, gyada kai ta shiga yi, sai kuma ta mika masa wani takardan tace "Prescribe for someone suffering from chronic stomach ulcer!" Karba yayi ya kuma rubuce rubucensa ya mika mata, ta karba tana dubawa tace "Um! Yayi kyau, kana theatre ne?" Yace "Ina yi Mami" ta basa wani takardan tace "Rubuta min procedure din yanda xa ayi operating din patient that's suffering from Appendix...." Karba yyi cikin yan mintuna ya gama ya mika mata ta karba tana kallo, murmushi tayi tace "Alryt Doctor, am offering you work at my clinic daga gobe, sai ka shirya da safe mu fita tare..." Ya buda ido yace "Am soo grateful Mamina" tace "My pleasure, but try to reconcile with ur parent kaji boy, kar mace ta hadaka da iyayenka" a hankali yace "In shaa Allah Mami" aikin da take yi a laptop ta juya masa gabansa tace "Idan baxan takura ka ba pls go on with this it's understandable, am already exhausted dama..." Yace "Alryt Mami" daga haka ya fara duba abinda take yi, duk abun nn da suke Fatima na lekensu don tun da taji muryarsa ta taho da sauri ta labe, tana ganin uwarta ta mike ta bar gun da sauri, Hajiyar na kallonsa tace "Xaka iya tafiya da shi boy, idan ka gama sae ka kawo min" yace "Alryt Mami," daga haka ya dau system din da takardun dake ajiye yayi mata sallama ya wuce, ita kuma ta shiga ciki, shara ya tadda samha tana yi a parlor ya girgixa kai ya xauna yace "Kin san me?" Ta kallesa ta ce "Mene?" Yace "Three things you never get tired of are, bathing, cooking and sweeping i notice" dariya ya bata sae dai bata yi ba tayi murmushi ta xauna tace "Toh sae ka tashi kayi" ya wara ido yace "Haba in tashi in yi" ta hararesa tace "Ehh" mikewa yayi ya nufi gun da ta ajiye broom din ta dauke da sauri kafin ya isa, karba yake son yi taki sake masa tace "Nooo, ka kyaleni...." *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 _Hafsat Ummu Ilham, i don't dedicate pages but here is a whole page for you dear sis, Am so grateful for the visit Allah ya bar xumunci sis ya raya su Ilham da Annur, Khaleesat heart you sisto_ 😍 36..... A can kano kuwa har gobe neman Abuturrab Abba yake, har imagining irin hukuncin da xae masa yake, Sosai Mami ta damu ganin har kusan sati bbu labari, to ina Aliyu xae kai yar mutane, kullum Hajiya Mariya sai ta xo gidan yayar tata tana kwantar mata da hankali amma ko kadan bata nuna tasan idan Aliyu yake ba duk da ta lura xargin ta yayarta take, Mahaifiyar Samantha kuwa ba don mai gidanta da ya hanata ba kotu dama tayi niyar kai karan, bata da aiki sae kuka da tsine ma Abuturrab ta kuma dau kudirin ko da ya dawo da Samantha kasheta kawai xata yi kowa ya huta don bata san mugun abinda yaje yyi mata, da dai ace ta xama musulma gwara ta kasheta a cewarta, bbu bata lkci ta shiga shirin tafiya Jerusalem don yin addu'an Allah ya dawo da Samantha tayi masa sacrifice dinta, mahaifin Samantha kam mutum ne mai saukin kai da boye damuwa baxa ka taba cewa abun na damunsa ba. Ranar Asabar Samha na kitchen tana kkrin daura girki da yamma shi kuma Abuturrab na xaune balcony rike da sabon system din da ya siya don bai iya rayuwa bbu shi, d'aga kai yyi ganin shadow din mutum, ya ga fatima tsaye daga bakin balcony din tace "Mum tace matar ka ta xo" daga haka ta juya ya bi ta da ido, haushin ta ya ji har cikin ransa, ko kadan yarinyar bata yi masa ba, ya ga alamar bata dau hali irin na mahaifiyarta ba sai girman kai, ya tabe baki ya mike ya shiga ciki, kallonsa Samha tayi jin abinda yace, can tace "Toh girkin fa!" Yace "Don't worry ki sa hijab ki tafi" ba musu tayi yanda yace ta fita xuwa part din Hajiya, tana parlor da duk 'yan matan nata uku sai wata dake xaune tare da fatima alamar kawarta ce, Samha ta risina ta gaisheta ta amsa da fara'a tace "Kadaici bai damun ki Samha, ki dinga shigowa nan ku saba da su fatima mana" murmushi Samha tayi tana wasa da fingers dinta tace "Toh" Hajiya tace "yauwa ko ke fa, xama ke dayan nn bbu dadi, ki dinga shigowa cikin mutane" kai samha ta gyada mata, Hajiya tace "Kar fa ki daura girki xa a kai maku idan an gama a nan kin ji" murmushi Samha tayi bata ce komai ba, Mami tace "Gobe su fatima xa su saloon sai ki bi su ki ga gari idan mijin ki ya amince, ke ma sai kiyi gyaran gashin daga can" Samha tace "Uhm to Mami" Fatima ta mike ta dalilin wayarta da yayi kara ta kalli kawarta Bilkisu tace "Gashi sun kira Billy" daga haka suka fita balcony, a waje Billy tace "Teemah new tenant din gidan nan ne yarinyar nn?" Fatima ta kalleta sae ta fasa d'aga wayar tace "Ehh" Billy tace "Kai amma yarinyar is pretty... Amarya ce koh?" Fatima tayi wani murmushi tace "Sai ma kin ga mijin xa ki san she is nt pretty...." Billy ta wara ido tace "Haba dai??" Fatima tace "Uhn He is more than cute, kin san Allah gabana faduwa yake idan muka hada ido da shi, but sai in wani daure fuska ko gaishesa bana yi" Billy tace "Waoww xan so in gansa kuwa" Fatima xata yi magana sai ga Samha ta fito ta sa takalmanta ganin yanda suke kallonta tace "Sannun ku" Billy tace "Yauwa!" Daga haka tayi wucewarta xuwa part dinsu duk suka bi ta da ido. Abuturrab yace "Har kin dawo?" Kai ta gyada masa tace "Tace xa mu je saloon gobe da yaranta" Shiru yyi yana kallonta sai kuma yayi murmushi yace "Allah ya kai mu" ciki ta shiga tayi kwanciyarta tun da tace kar tayi girki, fatima ce ta kawo masu abinci kusan Magrib bbu sallama ta shigo parlon, Abuturrab na xaune yana kallo a system Samha na gefensa ta jinginar da kanta jikin shoulder dinsa idonta a kan system din ita ma, a tare suka daga kai suna kallonta, ko kunya taji sai kuma ta sunkuyar da kai tace "Assalamu alaikum" Samha ce kawai ta amsa ta karaso ta ajiye abincin tace "Mum tace a kawo" Samha tace "Mun gode" daga haka ta juya ta fice. D'an tsaki Abuturrab ya ja can ciki, Samha ta kallesa tayi murmushi bata ce komai ba. Washegari khadija ce ta taho Balcony tana kallon Abuturrab dake duba newspaper da ya siya daxu da ya fita karo masu kaya a boutique, gaishesa tayi ya amsa tace "Wae Ummin mu in kira Anty Samha idan ta shirya" Abuturrab yace "Toh ga ta nan xuwa, ya sunan ki?" Tayi murmushi tace "Sunana khadija" yace "Alryt xan fadi mata Khadija" juyawa tayi ta wuce ya bi ta da kallo ganin banbancinta da yayarta, baxa ta wuce shekaru sha bakwai ba amma tafi yayar hankali, yana xaune parlor samha ta fito da hijab har kasa tana kallonsa, murmushi yyi yace "Cute" murmushin ita ma tayi, yace "Sae kun dawo but kar ki bari a dinga kalle min ke fa" dariya tayi yace "Yeah nikab ma xan siyo maki" kofa ta nufa ya bi ta da ido har ta fita, jiranta ta samu su Fatima na yi, Hajiya Hajarah tace "Toh sae kun dawo, Allah ya tsare hanya" driver ne xae kai su saloon din, fatima ta shiga gaban mota, Khadija da Rabi'ah suka xauna baya tare da Samha, su kadae suke mata hira har suka iso saloon din, fatima ta bude mota ta fita su ma suka fita suka bi bayanta xuwa cikin babban saloon din, khadija na kallon fatima tace "Big sis a fara yi ma Anty Samha koh?" Fatima ta kalli Samha ganin kallonsu take bbu yabo bbu fallasa tace "Alryt" daga haka taje tayi xamanta kan daya daga kujerun Saloon din sae dae can kasar xuciyarta ji take kamar ta shake yar uwar tata, Samha da Rabia aka fara ma gyaran gashin don akwae mutane saloon din, tun da aka bude kan Samha Fatima da duk yan saloon din ke kallo, matar mai gyara mata gashin sae cewa take "Maa sha Allah you've got a very fine long hair" Samha ta kirkiri murmushi bata ce komai ba sai dai duk a takure take ganin yanda ake kallonta, cikin minti ashirin aka gama mata ta mayar da hijab dinta da sauri, aka kama kan fatima sae dai ita kitso tace xata yi, ita din ma ba baya ba gun gashi, mai saloon din na kallonta tace "Baxa kuyi lalle ba Madam?" Khadija tace "Xa muyi" wani kallo Fatima ta watsa mata tace "ke da wa, waye xae jira kuyi lalle?" Khadija tace "Ae na tambayi Ummi tace mu yi" dauke kai fatima tayi bata ce komai ba, khadija aka fara yi ma snn Samha da taki yarda da farko har sae da Khadija da Rabi'a suka tilastata, suna saloon din har aka kira azahar, Khadija ta kalli Samha tace "Mu shiga daga ciki mu yi sllh Anty Samha" shiru Samha tayi sai kuma ta mike kamar mara laka ta bi bayanta, Khadija ce ta fara alwala a toilet ta fito snn Samha ta shiga, tsura ma tap din ruwan ido tayi, lkci daya xamanta gidan kanwar Abbanta ya fado mata, a hankali ta bude ruwan ta shiga alwalan kamar yanda take yi a kaduna da yaran Aunt dinta, tana gamawa ta fito ta ga Khadija ta shimfida mata wani darduma ta saka hijab dinta ta hau kan darduman babu abinda ta mance a ynda ake sllhn sae d'an abinda baka rasa ba, har hakan ya bata mamaki, tana idarwa Khadija tace "Me xa a karbo maki?" Murmushi Samha tayi tace "Bana jin yunwa..." Khadija bata ce komai ba ta fita, samha ta mike ta bi bayanta, snacks da drinks Khadija ta sa driver ya karbo masu, bbu yanda samha ta iya haka ta karba, ba su suka bar saloon din ba sai kusan karfe uku, part din su suka tafi gaba daya, Hajiya ta yi masu sannu da xuwa tana kallon Samha tace "Har kun dawo?" Samha ta gyada mata kai, tace "Toh sannun ku daughter, bari a xubo maku abinci" Samha tace "Ae mun ci" Hajiya bata saurareta ba tasa mai aiki ta xubo masu abinci gaba daya, har aka yi la'asar tana parlon, Hajiya tace "Khadija ku shiga ciki ku yi sllh" Khadija ta kalli Samha tace "Muje daki muyi sllh" ba musu Samha ta mike ta bi bayanta xuwa bedroom dinsu, kamar daxu haka tayi sllhn suka fito bayan sun idar, nan Hajiya tasa mai aiki ta xuba mata abinci ta kai ma Abuturrab, ta karbi abincin tayi godiya ta fita, Kwance ta samesa parlor yana bacci, ta ajiye abincin hannunta ta durkusa kusa da shi tana kallonsa tace "Doctor!" Bude ido yayi a hankali, ta langwabar da kai tace "Anyi sllh fa" ya mike xaune yana shafa fuskarsa, tace "Are you okay?" Girgixa mata kai yayi yace "Am having headache..." Tace "Toh kayi sllh sai kaci abinci then you take drugs" tana magana amma ido da hankalinsa na kan kunshin hannunta, ta bata rai tace "Ina maka magana" kamo hannunta yayi murya can kasa yace "Waow, baby kunshin yayi kyau sosai, i like it" ta kwace hannunta tace "Thanks" ya d'an marairaice mata yace "Toh baxan ga gyaran gashin ba?" Murmushi tayi ta cire Hijab din jikinta tana kallonsa, ya lumshe ido underneath his breathe yace "I have always loved you from the very first day i saw you Samha!" Kallonsa kawae take, ya bude ido a hankali yace "Tell me daga ina kike that very Night?" Murmushi tayi xata mike ya jawota jikinsa yace "Noo, talk to me baby" murmushin ita ma tayi tace "I don't want to talk about that now!" Yace "Noo plss baby..." Ganin yanda ya zuba mata manyan idanuwansa ta sauke kanta kasa a hankali tace "My frnd forced me to her birthday party, ni ban san it's an indecent party ba, shine na gudu na bar wajen..." Bude kofar parlon aka yi ta xame jikinta da sauri dai dai lkcn da fatima ta shigo, ta sunkuyar da kai ta karaso parlon, Samha ta xamo kasa a hankali ta xauna, takardun hannunta ta mika ma Abuturrab tana kallonsa tace "Ummi tace in baka wannan..." Mikewa yyi bbu yabo bbu fallasa yace "Drop it!" Daga haka ya shiga bedroom, ta bi sa da ido, Samha ta kirkiri murmushi da kyar ta karba tace "Bari in ajiye" sake mata fatima tayi ta juya ta fice daga parlon. Samha ta mike a sanyaye rike da takardun ta shiga dakin da ya shiga, xaune ta gansa gefen gado ta durkusa kusa da shi tace "Me yasa kayi mata haka?" *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By Khaleesat Haiydar📚✍🏻 _Tohm ya na iya tunda Ummu Ilham na da 'yan adawa irinsu Chamo, Zaarah, Teemahluv, Deezoh... Gasu nn dai🙄 su ma kuma sun ce sai fa an masu baxa su yarda ba, toh ina ku ke gashi nan sai ku kacalcala shi bbu ruwana naku ne_ 😆 37 Dagota yayi ya xaunar da ita gefensa yace "Kinsan me Baby?" Ta girgixa kai yace "Hajiya ta ban aiki...." Samha tace "Aiki kuma?" Yyi murmushi yace "Yeah she's also a medical doc...." Tace "Uhm hw did she know you re a doc?" Yar dariya yyi yace "Taga bana xuwa aiki shine ta tambaya nd i told her nayi ma Abbana laifi shi yasa na bar kano..." Xaro ido tayi tace "You told her everything??" Kamo hannunta yayi yace "No i didn't love!" Sunkuyar da kanta tayi, ya daura hannunsa kan dogon gashinta murya can kasa yace "Haka xa ki haifa min yara masu irin gashin nn kin ji" da sauri ta fara kkrin sauka daga kan gadon yaki saketa, kmr xata yi kuka tace "Doctor baka yi sllh ba fa..." Dariya yayi yace "Sai in tare xa mu yi bby" ta kallesa tace "Uhm ae yau na yi!" Yace "Dagaske?" Tayi murmushi tace "Yeah nayi Zuhur a saloon, nayi Asr a gun su Ummi" ya wara ido yace "Don Allah da gaske Baby, toh me da me kika ce a sllhn" wara ido tayi tace "Na fa ce maka ina yi a kaduna, rayuwar da nayi a kd a da yafi wanda nayi a kano da parent dina, am still missing my aunt, amma Mum dita ta rabamu wai she's putting me in the islamic way..." Abuturrab da ke ta kallonta yace "Toh me Abba yace?" Ta wara ido tace "Toh me xai ce? He said nothing, for the past 3yrs aunt dina bata xo gun mu ba..." Abuturrab yyi murmushi yace "Za mu kai mata ziyara knn" da sauri tace "Da gaske?" Yace "Yeah sweety, amma ba yanxu ba" daga haka ya mike yace "let me Ablute..." Washegari kamar yanda Hajiya tace da wuri Abuturrab ya shirya yana 'yan dube dube a laptop, aka danna bell, Samha dake goge gogen parlon ta mike ta isa gun kofar ta bude, khadija ce tsaye tayi murmushi ganinta khadija tace "Ina kwana Anty Samha" Samha tayi murmushi tace "Lafiya lau khadija" khadija tace "Ki ce ma Uncle Ummi tace tana jiransa fa" Samha tace "To" snn ta juya ta koma parlon tana kallonsa tace "Wae Ummi na jiran ka" mikewa yayi ya rufe laptop din ya langwabar da kai yace "Ko mu je tare ne baby, ke fa kadai zaki xauna gida" murmushi tayi tace "It's nothing ai na saba..." Yace "Alryt da wuri xan dawo kin ji?" Kai ta gyada masa ta rakasa har bakin kofa yayi peck din goshinta, ta juya da sauri ta koma parlon ya wuce yana murmushi, A parking space ya tadda ta tana jiransa, ya gaisheta ta mika masa car key din ya karba a xuciyarsa yace to da bai iya tukin ba fa, yana gama warming motar ta zaga ta shiga, duk wnn abun fatima na kallonsu ta window a daki, Ummi tace "Samhar fa?" Yace "Tana ciki Mami..." Tace "Duk xata ji bbu dadi ita kadae ga su fatima duk makaranta za su..." Murmushi yyi yace "Ae ta saba Mami" Sae da suka fita compound din tace "Ina matakin karatun ta ya tsaya?" Yace "Waec ta gama recently, but na kai ta tayi jamb registration nn garin" Mami tace "Good..." Daga haka ta dinga nuna masa inda xai bi har suka iso Clinic din, babba ne sosai asibitin, yana gama parking a space din da aka tanada don haka ta fito snn shi ma ya fita, ya bi bayanta xuwa reception, gaisheta nurses din dake gun suka dinga yi ta amsa ta nufi stairs xuwa office dinta, shi dai yana biye da ita har suka iso, Hadadden office ta shiga da shi, ta kunna Ac, ta yaye curtain snn ta xauna ta nuna masa kujera shi ma ya xauna, wayarta ta dauka ta kira wani likita, ba a dau lkci ba wani da baxae wuce Abuturrab ya shigo, ya gaisheta da ladabi ta amsa tace "A new doctor here, xa ayi employing dinsa a nn" Likitan me suna Shareef yace "Alryt, his qualificatios...." Ta girgixa kai tace "Forget that" ya gyada kai, snn ya juya ga Abuturrab ya basa hannu yace "Am Dr Shareef" Abuturrab ya karba hade da murmushi yace "Dr Aliyu" Dr shareef yace "Welcome to our clinic" Ummi tace "Office din kusa da naka xa ka bashi, idan Bashir ya dawo sai ya koma second flour" Dr Shareef yace "Alryt" daga haka ya kalli Abuturrab yace "Mu je Doctor" mikewa Abuturrab yayi yana kallon Ummi, ta dau makullin mota ta basa tace "Ba da dadewa ba xan fita meeting, when it's four sai kayi wucewar ka gida" yace "Toh ke fa Mami" tace "Akwai wani mota a nan xan fita da shi" yace "To nagode Mami" daga haka ya bi bayan Dr shareef suka fita, office din nasa madaidaici ne me dauke da table da office chair, snn da kujeru, sai show glass mai dauke da magunguna da injections a ciki sae gadon Anti Natal, da dai abubuwan da office din likita ke bukata, Dr Shareef yace "Hope you will like it here" Abuturrab yyi murmushi yace "In shaa Allah" Dr Shareef yace "Toh na bar ka lafiya" daga haka ya fita Abuturrab ya xauna kan kujera hade da lumshe ido. Kafin karfe daya patient din da yyi attending ma sun kusa goma, ana bude kofa ya hade rai, nurse din dai ce ta shigo da wani file kafin ta karaso yace "Ke doctors nawa ne a asibitin nn" kallonsa take bata ce komai ba, ya lura she derives pleasure looking at him, ya wani mugun hade rai yace "r you Daft?" Da sauri tace "Sir?" Kin cewa komai yyi yana kallonta fuskar nn tasa kamar hadari, tace "Amm, amm Doctors shidda ne sir...." Yace "Toh kar ki sake shigo min da file.... Fita" juyawa tayi ta fita, ya ja tsaki shi haushin irin kallon da take masa ma yake kawai. Kamar yanda Mami tace ana Asr yyi ma Dr shareef sallama, har ya kai bakin kofa ganin kallon da nurses din ke masa gaba daya ya juyo ya dawo, yace "I am Dr Aliyu, am gonna work here with you all for the mean time, yeah am very free nd friendly amma bana son kallo don Allah..." Daga haka ya juya yayi ficewarsa, wasu suka bi sa da harara, wasu kuma kamar idanuwansu xa su rakasu har gun motar. kusan a tare suka shiga compound da fatima a tata motar, yana gama parking a space dinsu ya kashe motar ya fito, ita ma ta fito da kawayenta biyu, ko kallon inda suke bai yi ba ya juya ya nufi part dinsa, duk suka bi sa da ido, Salima tace "Kaddai ku ce min shi ne" Fatima bata ce komai ba ta dau hanyar balcony dinsu, Billy ta sauke ajiyar xuciya tace "Shine mana" daga haka suka bi bayan fatima Salima na ta waigan Abuturrab da har ya isa part dinsa. Khadija dake parlor da Samha ta mike da sauri ganinsa tace "Sannu da dawowa Uncle" yayi murmushi yace "Yauwa khadija, how you?" Tace "Fine," Daga haka ta nufi kofa yace "Ina xa ki kuma" tace "Dama xan wuce ne" yace "A'a xo kiyi xaman ki" Shiru tayi bata ce komai ba ya kalli Samha yace "Ina yini Ma" murmushi tayi tace "Sannu da dawowa" yace "Thanks dear" daga haka ya shiga Bedroom, khadija ta dawo tayi xamanta parlon tana ci gaba da ba Samha lbrin da take bata. Kwance Abuturrab yyi Maminsa a ransa, haka kawai ya tashi da ita yau yaji ganinta kawai yake son yi, can ya mike xaune ya dau wayarsa, yyi jim kmr me nazari kafin yayi dialing numberta, yana fara ring gabansa ya shiga faduwa, Mami dake parlor ta rungume hannaye tana sauraren tijaran yakumbo, ba ayi ranan da xae wuce bata xo ta xaxxaga mata tsiyar ta fito da Aliyu ba, a da tana addu'ar Allah ya karkato hankalinsa ya dawo gida ko don xarginta da ake a kan tasan inda yake, amma yanxu kam addu'a ma take kar ya dawo don tasan duk inda yake he is fine don ya saba irin haka, matsalar daya ynxu da yar mutane da ya tafi banda haka ya shekara ma bai dawo ba in dai yana lfya ko a jikinta, dai dai nn wayarta ya shiga ring ta jawo da yake neman hanyar da xata bar parlon take duk da bakuwar number ne hakan bai hanata dauka ba upon maganar da yakumbo take cikin dag'a murya, Abba dai sai operating laptop yake, sallama Mami tayi Aliyu yyi shiru jin muryarta, har sai da ta sake maimaita sallaman, da kyar yyi gathering courage yace "Mami..." Sosai gabanta ya fadi jin muryarsa, ta mike ta kuma yin sallama kamar bata ji sa ba ta nufi stairs, a fusace yakumbo tace "Ahmad dubi ni ta tsallake ta wuce ina mata magana...." Abba ya kalli Mami da har ta kai stairs yace "Hajarah!" Ba tare da ta kallesu ba tace "Ina xuwa, Gwaggo na ce ke kira" daga haka ta wuce sama, Abba ya d'an kalli Yakumbo yace "Tana xuwa yaya..." Tabe baki tayi tace "Ta matse mata can, wato Ahmad ynxu shknn haka xa mu xuba ido an kasa sanin inda Aliyu yake, ni tsorona daya fa kar yaje masallaci a aura masa kafura mu shiga uku..." Sai ta fashe da kuka tace "Wllh Ahmad kaf xuri'ar mu kai ma kasan bbu tubabbe, wnn wace irin kaddara ce haka, mu Aliyu xae xuba ma duwatsu a ido, mu xae kunyata, mu xai toxarta?? toh wllh yyi kadan ko da ya auri yarinyar nn ko bayan raina sai an raba auren, mu xai haifa ma jikokin jaraba? Matsawar ina numfashi wllh wllh bbu aure tsakaninsa da tsinanniyar, ko ya aureta kuwa sae ya saketa, bare kullum axumi nake ina roko kada Allah ya basa ikon aurenta...." *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By Khaleesat Haiydar📚✍🏻 Tohm where r u my Fertymerh Zahrah and Ummi Aysha.... ku ma ga naku shuwagabannin Haske, Allah ya kara mana basira baki daya😍 38..... Tun da ta fara Abba ya tsaida abinda yake yana saurarenta, tana kai wa aya kuwa tace "Ko ya ka ga?" Ya gyada kai yace "Haka ne!" Mami na shiga dakinta ta rufe kofar tace "Aliyu!!" Ya lumshe ido cikin sanyin murya yace "Forgive me plss Mami, i know i disappointed you, ki yafe min don Allah..." Tace "Kana ina yanxu?" Shiru yyi, a fusace tace "Baka ji na ne?" Yace "Mami don Allah kiyi hakuri, ina... Ina kaduna..." Tace "Karya kake Abuu, ina yar mutane?" A hankali yace "Tana nan Mami..." Mami ta girgixa kai tace "Yanxu rayuwar da ka xabar ma kanka kaga shi xae fishsheka Abuturrab, warce ba muharramar ka ba kake rayuwa da ka ajiye koyarwar addinin ka aside?" Shiru yyi bai ce komai ba, tace "Aliyu..." Nan ma dai bai ce komai ba, ta kuma san yana jin ta baxae dai yi maganan bane, tace "Toh yanxu meye amfanin haka Abuu, me yasa har gobe baxa ka dawo gentleman ba?" Xaunawa tayi gefen gado ta dafe kanta, can tace "Look kayi min magana ynxu bana son wlknci, tell me what's the meaning of what you did?" Ya bude idonsa dake rufe da kyar yace "I want to convert her...." Mami tayi tagumi tace "Ta haka ake converting din mutum Aliyu, ka dauketa ku gudu kamar wani Indian film kace min you want to convert her?" Murmushi yyi cikin sanyin murya yace "Kiyi hakuri Mami, ke ma kinsan ynxu idan na dawo da matsala, mami you've got to trust me, kinsan abinda xanyi da wanda baxan yi ba, ni bana fasikanci kin sani, just that this the only way out, xan dawo gida in shaa Allah amma har sai naga hankalinta gaba daya ya karkata ga islam, nasan duk abinda nayi ma 'yar wani surely xa ayi ma nawa kidz din kuma har kannina xai iya shafa sbda haka am very cautious of what i do...." Mami tace "A ina ku ke ynxu?" Yace "Muna Gombe Mami" ta xaro ido tace "Wa ka sani a can Abuu?" Yace "Bbu kowa gashi kuma har nasan mutane ynxu har na fara aiki" tace "Da wani CV din??" Yayi murmushi yace "Da na brain dina Mami" Mami tace "Aliyu ka rufa min asiri ka mayar da yar mutane, Aliyu ni wnn abinda kke son yi ko kadan bai gamshe ni ba, yanxu rayuwar nn wa kaga xae yrda xuri'arsa a samu irin haka, ba fa ce maka tayi tana sha'awar addinin ka ba, kai ke cusa mata kawai, gaba nake jiye maka wllh, shawarata kawai ka dawo in taga tana son musulunci xata yi ne ba sbda kai ba... Ka dawo kayi auren da iyayen ka ke son kayi Abuu, ka ajiye shashancin nn da kake yi son" da damuwa yace "Mami ni wllh ita kadai naji xan iya aure... Pls ki bani go a head ko yanxu xan iya aurenta nasan zata amince kuma dawowa addinina baxae mata wahala ba in har na aureta" Mami tace "Toh ba da yawuna ba wllh, in kuma shakiyancin naka har ya kai ka fara tsallake magana ta to bismillah, na fada na sake fada ba da yawu na xaka je a daura maka aure da Christian ba...." Daga haka ta katse wayarta, ya rike kansa. Can ya mike da kyar ya cire shirt din jikinsa ya kwanta kan gado hade da lumshe ido, ya fara bacci samha ta shigo dakin, durkusawa tayi kusa da shi tana kallonsa a hankali tace "Doctor..." Bude ido yyi don baccin nasa bai yi nisa ba, tace "Abinci fa?" Ya mike xaune yace "I've eaten sai anjima" tace "Toh..." Mikewa tayi xata fita yace "Samha!" Ta koma ta durkusa tace "Na'am..." Ganin kallonta kawai yake tace "Doctor i prayed today also..." Yace "Really?" Tace "Yea, tare da khadija, she came back from islamiyya around 1, shine ta xo nan... Tace min ita ma recently tayi waec" Yace "Waow, shknn kin samu frnd knn... Which means you weren't lonely today!" Tace "Yeah, tare muka yi girki da ita, i like her she's very nice" yace "Uhnn! Ai naga alama" ta langwabar da kai tace "Toh ko nima in dinga bin ta islamiyyan i don't want to be staying at home all alone kafin ta dawo" ya sauko da kafafuwansa yana kallonta yace "If that's what you want love sai in sa ki..." Tace "Ehh ina so!" Yyi murmushi yana kallonta yace "Alryt gobe sae ki fara koh?" Ta gyada masa kai, mikewa tayi tace "Let me go back tana parlor, nayi xaton xaka ci abinci ne" yace "Am ohkay dear, ltr xan ci" tace "Tohm" snn ta fice daga dakin ya bi ta da ido murmushi dauke fuskarsa, sosai yaji ddin islamiyyar da tace xata, and he was happy she brought the idea her self. Washegari yana dawowa daga masallaci ya shiga dakin da take ya tada ta, ta mike xaune tana mitsike ido yace "Yau baxa kiyi sllhn ba knn?" Ta kallesa tace "Sllh kuma?" Ya wara ido yace "Alryt dear, yi kwanciyar ki nayi xaton xa kiyi sllhn ne" bata ce komai ba hakan yasa ya juya ya nufi kofa, mikewa tayi ta bude kofar bayi ya juya ya kalleta bai dai ce komai ba ya fita ya shiga wani dakin don shiryawa tunda yyi wanka kafin ya je masallaci yana buttoning din shirt dinsa ta shigo da hijab jikinta, ta karasa dakin tana kallonsa tace "Nayi sllhn" yace "That's very nyc of you love... Allah ya karba" murmushi tayi tace "Me xan yi maka for brkfst?" Yace "Just lipton xa ki dafa dear, akwao bread" tace "Kwai fa?" Yace "Noo, ni baxan ci ba sai dai ke" juyawa tayi ta fita, ko kafin ya fito har ta dafa ruwan Lipton din ta ajiye a parlor da kayan beverage, ya karaso parlon ya xauna ta hada masa tea'n yana kallonta, ganin irin kallon ta sunkuyar da kanta, murmushi yyi ya jawo cup din tea din, tace "Baxan je islamiyyan ba yau?" Yace "Xa ki mana baby" mikewa tayi tace "Tohm bari in shirya" daga haka ta shiga daki, yana gamawa ya fita xuwa part din Hajiya, karo ya kusa ci da fatima da ta fito daga parlon hannunta rike da makullin mota tana sakale da jaka alamar boko xata, Bai ko kalleta ba ya bi ta gefenta ya isa kofar ya danna bell, kin tafiya tayi ta xuge jakar hannunta tayi pretending kmr neman abu take, Khadija ce ta bude kofar ta gaishesa da fara'a ganin shi ne, yace "Mami fa?" Tace "Tana ciki bari in mata magana" daga haka ta juya ta koma parlor, ba a dau lkci ba ta dawo tace "Wai ka shigo" Bin bayanta yyi suka shiga parlon, dai dai lkcn da Mami ma ta shigo parlon, xauna yyi kan sa a kasa ya gaisheta ta amsa tana murmushi tace "Kun tashi lfya Boy?" Yace "Alhmdllh Mami" tace "Har ka shirya knn, in dai ka gama abinda kke tun da akwai makullin mota gun ka sai ka dinga wucewa kawai boy" yace "Toh Mami, dama samha ce ke son shiga islamiyyar su khadija, ina son in fara xuwa can da ita ne...." Mami tace "Maa sha Allah, kace mata in dai ta shirya ta xo sai in kai ta.... Kai kayi wucewar ka kawai" A hankali yace "Toh nagode Mami" daga haka ya mike ya fita duk da hakan bai gamshe sa ba don bai son Mami tasan bata san komai ba. Fatima dai na nn tsaye fa har lkcn, wnn karan tare masa hanya ma tayi duk don yyi mata magana, ga mamakinta sai gani tayi ya tsallake karfen dake xagaye balcony din yyi wucewarsa. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 Hmm where are you blood!😍 Ke ma ga naki, Allah ya kara hada kawunanmu sweet sis Iqram Mujaheed (Maryam M Bello) proud to have a sister like u. 39..... Parlor ya tadda Samha yace "Dear ki shirya Mami xata ajiye ki a islamiyyan...." Shiru tayi tana kallonsa, ya kamo hannunta yace "Yea, i wanted taking u there by my self but she insisted...." Ta langwabar da kai a hankali tace "Toh" mikewa yyi yace "Yauwa baby, sai ja dawo" tace "Allah ya tsare...." Har ya kai bakin kofa ya juyo yace "Bbu rakiya dear" murmushi tayi ta mike ta bi bayansa suka fita a tare, hada ido suka yi da fatima dake tsaye tsakar compound din ta kasa tafiya, Samha ta kirkiri murmushi tana kallonta tace "Good morning sis fatima" Fatima ta mayar mata da yake tace "Same" daga haka ta nufi gun motar ta da take xuwa makaranta da, Shi dai Abuturrab bai ko kalli inda suke ba har ya isa gun motar da Hajiya ta basa ya juyo yana kallon Samha da ta bi bayansa, jawota yyi gabansa yana kallonta yace "Tohm sweet sai na dawo" murmushi tayi ta gyada masa kai, har xai kai bakinsa nata ko me ya tuna kuma ya bude mota kawai ya shiga tana tsaye ya gama bata wuta snn ya kalleta ya kashe mata ido ya ja motar hade da horn mai gadi ya bude masa gate, Kallon motar fatima kawai Samha take har ita ma ta fita da gidan, ta kusa minti uku tsaye tana kallon gate din gidan snn ta juya da kyar ta koma ciki. Cikin d'an lkci Abuturrab ya saba da doctors din clinic din bayan sun fito daga theatre a ranan, barin da suka ga shima kwararre ne, few nurses da yaga alaman suna da hankali kadai ya sake ma, sai dai fa throughout ranan duk da uban aikin da yyi hankalinsa gaba daya na kan maganganun Maminsa da ya tuna sai gabansa ya fadi, shi dai yasan he can't do without Samha, gashi dai duk rashin jin sa baya tsallake maganan Mahaifiyarsa sai dai by mistake, tunanin yanda xai shawo kanta kawai yake amma bai san taya ba, karfe biyar ya bar clinic bayan ya gama abinda yake, hadari ne sosai garin me hade da iska ya shiga mota ya dau hanyar gida, tsaye yyi da motar bakin gate yana jiran motar da ya tarar gate din ya shiga, cije yatsa yyi cike da takaicin clashing din da suke yawan yi da fitsararriyar nn a cewarsa, gani yyi ta ki tafiya bayan gashi ta danna kan motar compound din, mai gadi dai ya koma yyi xamansa, can kuma dai ta ja motar ta shiga, ya yyi tsaki ya bi bayanta yyi part dinsa, yana gama parking ya fito yana satan kallon motarta ganin irin parking din da tayi, har lkcn iska ake yi sosai ga yayyafin da aka fara, har ya nufi part dinsa ya juyo da sauri jin sound din da yyi kama da na faduwa, kallon mamaki ya shiga yi mata ganinta a kasa, ganin she's gasping for breathe ae bai san lkcn da ya nufeta da sauri ba, yana isa gabanta ya durkusa ya dagota, a dai dai lkcn da Samha da Khadija suka fito daga parlor jin tsayuwar mota, daukarta Abuturrab yyi ya nufi cikin parlor da ita da sauri don an fara ruwan sosai, Khadija ta xaro ido tace "Innalillahi, Her inhaler....." Daga haka ta yi part dinsu da sauri ita ma, ita dai Samha bin su da ido tayi, Abuturrab ya kwantar da ita nan tsakiyar parlon yana kallon khadija da ta shigo yace "Me ake bata?" Khadija ta nufi daki da sauri tace "Inhaler dinta..." Yana rike da ita Khadija ta fito kamar xata yi kuka tace "Ni ban san inda ta ajiye shi ba, ina ta dubawa...." Abuturrab na kallonta yace "Ina inhaler din ki?" Bai ga alamar ta ma san yana yi ba don she is fighting seriously to get her breathe, Abuturrab yace "Inhaler kadai take amfani da, ba a mata allura ne?" Khadija ta girgixa kai tace "A'a ba ayi, sai magani da inhaler...." Da gudu ta koma daki dubo maganin sai ga ta ta dawo a rikice tace "Ni ban gani ba wllh" Abuturrab ya ciro waya ya mika mata yace "Kira Mami yanxu" daga haka ya daga ta ya xaunar da ita ya cire mata veil din da tayi roll a kai, Ummi na daukar wayar Khadija tace "Ummi Asthman Sister ne ya tashi ban ga inhaler ba" Ummi tace "Subhanallah, where did she keep d inhaler kin duba motar ta, where is she now?" Khadija tace "Uncle ne ya shigo da ita yace in kira ki, let me check d car" Ummi tace "Alryt yi sauri ki duba ba shi wayar" Mika ma Abuturrab wayar tayi, ta fice da sauri duk da ruwan da ake xuwa gun motar yayar tata, Ummi tace "Hello Doctor, wai ba a ga inhalern ta ba koh?" Abuturrab yace "Eh Mami, ba ayi mata allura ne?" Tace "Ban fiye son alluran bane son, but idan ba a ga inhalern ba bari in kira clinic yanxun nn a kawo mata alluran..." Daga haka ta katse wayar, ya ajiye ya jinginar da ita jikin kujera yana kallonta yace "Where is ur inhaler?" Dawowa khadija ta kuma yi tace "Ni dai bn gani ba ka kara kiran Ummi plss" daukar wayar yyi ya kira mum din tasu kuma, tana dagawa tace "Na sa Dr Usman ya taho da allura ynxu, he is on his way, kafin ya xo you tell khadija to check my room gun da nake ajiye drugs ta kawo maka magungunan sai ka cire wanda xa ka bata..." Abuturrab yace "Alryt" ya kalli khadija ya bata sakon ta nufi dakin, tana fitowa da drugs din ya dudduba ya dau wanda ya kamata, ya karbi ruwan da khadija ke mika masa, maganin ya kai ma fatima baki snn ya bata ruwan yana kallonta, daga haka ya jinginar da ita jikin kujera, yana nn durkushe gabanta Khadija kuma na tsayr kansu Dr Usman ya kwankwasa kofar parlor, khadija ta karasa da sauri ta bude kofar ya shigo yana kallon Abuturrab da ya karbi ledan hannunsa yace "Har ynxu ba a ga inhalern ba?" Abuturrab na kokarin hada alluran yace "Yeah!" Yana gama hadawa ya kalli fatima da har lkcn numfashinta bai dawo dai dai ba, mika ma Usman Alluran hannunsa yayi yace "Ga shi kayi mata" Usman yace "Noo kai mata kawai mana" mikewa tsaye Abuturrab yyi ya kama hannun Usman ya saka alluran a ciki yace "Kayi mata doctor, ina xuwa yanxu" daga haka ya nufi kofa, Usman ya durkusa don yi mata alluran, part dinsa ya nufa cikin ruwan, har lkcn Samha na tsaye balcony, Murmushi ya sakar mata ya isa gabanta yace "What r u doing here baby?" Juyawa tayi bata ce komai ba tayi shigewarta ciki, ya d'an yi jim, sai kuma ya bi bayanta, kwance ya sameta parlor ya xauna daga gefenta yace "Abun yar shariya ce kuma dear" ba tare da ta kallesa ba tace "Welcome" ya d'an yi murmushi ya mike yace "Thank you" daga haka ya shiga bedroom, sauya kayan jikinsa yyi xuwa jallabiya ya fito parlor, tana ganinsa ta rufe ido kamar mai bacci ta juya baya, ya nufi inda laptop dinsa ke ajiye a parlon ya dauka ya xauna kan kujera ya bude, bai yi minti goma parlon ba aka danna bell ya mike ya isa kofar ya bude, Dr Usman ne tsaye yace "Doctor nayi mata alluran, da sauki jikin nata yanxu, i want to leave now" Abuturrab yace "Alryt Doctor, let me check on her again, sai gobe" daga haka suka yi sallama Dr Usman ya wuce, tsaye Abuturrab yyi bakin kofar, can ya juya ya kalli Samha da har lkcn bata juyo ba bare ta bude ido, fita yyi parlon ya ja kofar, Cikin ruwan ya shiga xuwa part din Hajiya, Khadija na xaune gefenta ta lullube ta ita kuma tana kwance kan kujera, karasawa yyi parlon yana kallonta, ba karamin tilasta kansa yyi wajen ganin ya bude baki yace mata "How you feeling?" Sae a snn fatima ta kallesa, sai kuma ta dauke kai ta gyada masa kai kawai alamar fyn, shiru yyi kmr me tunanin abinda xai ce kuma, can dai ya kalleta suka hada ido, kasa cewa komai yyi, yyi saurin dauke nasa idon ya kalli Khadija yace "Yaushe Mami xata dawo?" Khadija tace "Tace tana hanya ynxu" yace "Alryt," daga haka ya kuma satan kallon Fatima nn ma suka hada ido ya juya xai fita daga parlon yaji tace "Thank you..." Ya kalleta bai ce komai ba yyi ficewarsa. Part dinsa ya koma, wnn karan Samha bata parlor, ya shiga daki ya ganta kwance idonta rufe, juyawa yyi ya koma parlor, yyi ta xamansa yana operating laptop har aka kira Magrib, alwala yyi ya fita xuwa masallaci don ruwan ba sosai ake yi ba, ko da ya dawo ci gaba da abinda yake yi yayi, karfe takwas saura aka danna bell ya mike ya bude kofar ya ga Ummi tsaye tace "Son nagode kwarai fah" yace "Mami ae da kin kirani in xo cikin ruwan nn kika fito" tace "It's not heavy ae, ina Samha" yace "Tayi bacci Mami..." Tace "Alryt, Allah bar xumunci, I don't just knw what's wrong with fatima da xata dinga yasar da Inhaler dinta anyhow..." Murmushi yyi yace "Allah ya tsare gaba Mami" tace "Ameen, Allah ya tashe mu lfya" daga haka yyi mata sallama ta juya ta wuce ya koma ciki. Karfe goma ya shiga kitchen bai damu da abincin dake ajiye kitchen din ba kuma yasan na shi ne,ya hada tea kawai ya fito parlor, yana gama sha ya shiga second room, ruwan wanka ya hada a bathroom yyi ya fito yyi shirin bacci yyi kwanciyarsa. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 Kawayen Asali Maman Shakur and Fiddausi s Dangi Jiddoh na gaisuwa, ku sani ku na raina a ko da yaushe😘 40..... Kasa bacci yayi ya rasa dalili, har karfe sha biyu da rabi idonsa biyu, mikewa xaune yayi daga karshe ya jima a xaunen kafin ya tashi ya nufi kofa ya fita, dakin da take ya karasa, ya kusa minti uku tsaye kafin ya tura kofar a hankali ya shiga, kwance ya sameta cikin bargo, ya karasa gefen gadon ya xauna yana kallonta, can ya sa hannu a hankali ya cire bargon, bai kai ga gama cirewa ba ta rike, kallonta ya tsaya yi can ya fixge gaba daya yace "Are you okay?" Mikewa tayi xata sauka daga kan gadon ya rikota yace "You re going no where har sai kin gaya min d reason for ur sudden change of behavior today, what's wrong with you?" Wani kallo ta watsa masa da yasa shi buda ido, ta kwace hannunta tace "That's because i want to be left alone...." Sai kuma ta fashe da kuka tace "Look Aliyu, you take me back to my parent immediately, i don't want any of this anymore...." Fixgota yyi yana mata wani irin kallo yace "Amma dai bni nasa ki taho gidana ki same ni ba that very night ryt?" Tsayawa tayi tana kallonsa ko kiftawa bbu, ya sake ta ya mike ya fice daga dakin ta bi sa da ido, har karfe daya tana nn xaune yanda ya bar ta ko motsi ta kasa, da kyar tayi karfin halin mikewa daga karshe, ta dau Hijab ta saka ta nufi kofa ta bude ta fita xuwa parlor, bata yi xaton ganinsa a parlorn ba, kuma suka yi ido hudu don kwance yake kan 3 sitter, ta dauke kai ta nufi kofar parlorn da sauri, mikewa yyi tana ganin haka ta ja kofar taji sa a rufe tana kkrin budewa da makullin jiki ya karaso ya fixgota, wani ihun da ya ji har tsakiyar kan shi ta saki tana son kwace kanta, ya rungumeta ya rufe bakinta da hannunsa yace "Meye hakan kike yi? Are you on ur right senses" Kokuwa ta dinga yi da shi tana son freeing kanta da bakinta a hannunsa amma ta kasa don wani irin rikon da yasa ko motsin kirki bata iya yi yayi mata, gajiya tayi tayi give up, sai a snn wasu hawaye masu xafi suka dinga xubo mata, duk jikinsa yayi sanyi a hankali ya saketa ta sulale nan gabansa ta fashe da wani matsanancin kuka, xubewa yyi gabanta kan gwiwowinsa shi ma, da kyar yayi karfin halin cewa "I didn't mean it Samha, forgive me plss i don't know what came over me...." Mikewa tayi da sauri ta kuma nufar kofar shi ma ya mike tsaye tun kan ta isa ya rikota, duka ta dinga kai masa cikin kuka tana cewa "Ka bude min pls i am going back to my parent, let me out immediately, xan maka ihu idan baka bude min ba" toshe bakinta yayi ganin da gaske ihun xata kuma yi, ya d'aga ta kamar yar shekara biyar yayi bedroom da ita ya direta kan gado yace "Pls you stop all this Samha and listen to me, am vey sorry don Allah kiyi hakuri i mean none of what i said to you....." Bbu irin lallashin da bai yi mata ba amma kamar yana d'a d'a tunxurata, sosai yake jin kukan da take har cikin ransa, wanda hakan yasa bai yi wani tunani ba ya kai bakinsa nata, nan ma dai ba karamin kokuwa tayi da shi ba amma lkci daya yasa ta nutsu, Tun yana yi don lallashi har abun ya fara wuce gona da iri, lkci daya ta fara kokarin kwatar kanta amma ta kasa don Abuturrab yayi nisa, xaro ido tayi da duk karfinta ta kwace bakinta cikin rawan murya tace "Don Allah kayi hakuri doctor ka sake ni, what's all this" doctor kam bai san tana yi ba, lkci daya ta fashe da kuka cikin rawan murya tace "Na shiga uku, Aliyu pls stop this am begging you, pls stop...." Da kyar murya can kasa taji yace "Pls Samha, you know... You know i... i love you..." Gigicewa tayi tace "Wayyo Mumy na shiga uku, don't Aliyu, i followed you because i trust you. Don't betray my trust for you.... Na yarda da kai...." Sama sama ya dinga jin abinda take cewa wanda hakan yasa jikinsa yayi sanyi amma ya kasa hana kansa, ji yake kamar his life depend on this, he just can't let go of her, cikin wata iriyar murya da ba tasa ba yace "Trust me Samha, auren ki fa xan yi..." Tana kuka sosai tace "Baka aure ni ba tukun doctor, don Allah ka tausaya min ka bari, ka daina plsss" Doctor fa yayi nisa bai jin kira, ba din daukewa da numfashinta ke kkrin yi ba tsabar tsoratar da tayi a lkcn da Samha fa an fita daga lane din da ake, ba shiri ya dawo Abuturrab dinsa sai dai duk jikinsa ya mutu, lallashin nata ma ya kasa, yana kallo ta mike ta fada bathroom, bayan kusan minti goma yaji karfi ya xo masa yayi karfin halin mikewa ya nufi bathroom din, murda kofar yyi yaji a rufe, ya jingina jiki ya lumshe ido cikin sanyin murya yace "Open pls Samha, kiyi hakuri don Allah, i never meant that too..." K'in budewa tayi kuma bata ce masa komai ba sai dai yana jin sheshshekar kukanta, ya durkushe wajen ya dafe kansa da yayi masa nauyi da ya sani kawai yake a lkcn, what came over him ma yayi haka duk daurewa da shan pills da yake ga yawan tsayuwar dare, ji yayi ya tsani kansa lkci daya, bai ma san me xai kuma ce mata ba, ya fi awa biyu bakin kofar amma taki budewa daga karshe ya mike gwiwa a sake ya karasa kan gado ya xauna, yanda bai yi bacci ba daren nn haka ita ma bata yi ba, ana kiran sallah ya fita ya koma daya bedroom din, wanka yyi ya dauro alwala ya fito yayi raka'atainul fajr sannan ya fita xuwa masallaci har ya dawo Samha bata bude bayin ba, gashi duk keys din har da spare a gu daya suke, ganin gari ya fara haske ya sake komawa dakin nn ma bbu lallashin da bai yi ba amma ta ki cewa komai kuma ta ki bude masa, xaunawa yyi gefen gado yana tunanin abun yi kuma, bakwai da kusan rabi ya mike da kyar jiki a sanyaye ya fita, part din Hajiya ya tafi, ya danna bell mai aiki ta bude, ya amsa gaisuwarsa yace "Hajiya na ciki?" Tace "Ehh tana nn" yace "Kiyi min sallama da ita" juyawa tayi ta koma, bayan kusan minti biyar ya ji muryar Hajiya na cewa "Boy ka shigo mana" ya shafa kai yace "Ba jimawa xan yi bane Mami..." Mami ta karaso bakin kofar ya gaida ta da ladabi ta amsa yace "Ya mai jiki?" Tace "Alhmdllh ga ta cab tana breakfast ne ma" yace "Toh Allah ya sauwake..." Tace "Ameen boy" ya na ci gaba da shafa kansa yace "Mami dama wata yar magana xa mu yi dake if you re free pls" tace "Toh shigo daga ciki mana" Yace "A'a Mami idan ba takura i wanted mu yi shi a can ne" ya nuna balcony dinsa, Mami tace "Alryt... Mu je" daga haka suka nufi balconyn a tare, ta ja kujera ta xauna tace "Toh ya aka yi son?" Xaunawa yyi, ya d'an yi shiru sai kuma yyi kasa da kai yace "A kan Samha ne Mami" Mami ta tattara hankalinta gaba daya tace "What about her boy, laifi tayi maka ne?" Ya girgixa kai yace "Mami ba dauke ki matsayin mahaifiyata da na baro a kano, don haka baxan boye maki komai ba, amma Mami this is a secret between us...." Mami ta gyada kai tace "Ina jin ka?" Ba karamin karfin hali yyi wajen cewa "Mami Samha fa ba matata bace!" Wani kallo Hajiya ta shiga yi masa daga sama har kasa kamar bata fahimce abinda yace ba, ya dafe kansa yace "Yea Mami sai dai kuma ba xaman fasikanci nake yi da ita ba Allah ma ya shaida..." Ita dai Hajiya har lkcj kasa cewa komai tayi da ganinta kasan ba wai mamaki kadan tayi ba, ya girgixa kai da kyar yace "It's a long story Mami... And Samha ba musulma bace Mami, hasali sunanta Samantha ni ne na mayar Samha..." Buda baki Hajiya tayi tana kallonsa da mugun mamaki, ya gyada kai a hankali yace "Ehh Mami" Hajiya tayi karfin halin cewa "Aliyu???" Bai dago ya kalleta ba ya ci gaba a sanyaye yace "Gidan iyayena is just few houses away from her parent's... That is layi daya muke, My father is a soldier My mum a lecture then, Samantha was born nd brought up in a strong Christian home, mahaifiyarta Pastor ce, her dad a politician...." *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 41...... Cikin sanyin murya yace "Duk da layi daya muke da Samantha ni bn taba lura da ita ba sai watarana da daddare....." Nan Abuturrab ya shiga ba Hajiya Hajarah labarin tun daga farkon haduwarsu da ita har ixuwa ranan da suka bar garin kano tare, Hajiya bata samu bakin cewa komai ba da ganinta kasan kanta ya gama daurewa haka ta tsaya kallonsa baki bude, ya ci gaba kansa a kasa har xuwa abinda ya faru jiya bai boye mata komai ba sai dalilin fushin da Samha tayi, Sai a snn Hajiya tace "Ya salam! Haba Aliyu duk ilimin ka ynxu kake xaune da warce ba muharramar ka ba, why boy, ynxu ba don Allah ya tsare jiya ba me kke tunanin xae faru, me yasa ka ajiye koyarwar addinin ka sbda son xuciya?At d first place ma meye na guduwa da yar mutane ka xabi toxarta iyayen ka, wato kai ba indiye koh?" Da damuwa yace "Mami ko da ma ban gudu da ita ba nasan baxan ji dadi gun Abbana ba, everything just happened all of a sudden, sannan ni Mami bn jin xan iya rayuwa da ita, i just can't do without her, and i notice tana da interest for islam, musuluntar ta baxai wani dau lkci ba, kuma ni aurenta nake son yi Mami, ni ko ...." Mami ta mike a fusace tace "Rufe min baki malam, is she still inside d bathroom" kai ya gyada mata tace "Wani dakin?" Yace "By the left..." Shiga parlon tayi tana mamakin karfin hali irin na Aliyu ynxu ashe duk wnn abun yarinyar nn ba matarsa bace, wai ba ma musulma bace, sai dai kuma abinda ya burgeta game da shi yanda yyi iya kkrinsa na ganin bai yi sabon Allah ba cos she can see he is very sincere, tunda gashi a dalilin abinda ya faru jiya yasa ya buda mata cikinsa, tausayin Samha ya shigeta sosai, ita kuma sbda soyayya ta yarda ta yasar da iyayenta ta ajiye addininta ta bi namiji bata san duk yanda Namiji yake to fa shi ba d'an goyo bne, sai dai all the same she is happy for her don da alama conversion dinta xuwa addinin gaskiya baxae yi wahala ba, tana isa dakin ta karasa kofar bayin cikin sanyin murya tace "Samha open the door, it's me" Samha da ke xaune bathroom din har bacci ya fara daukarta ta bude ido da sauri ta mike tsaye, Hajiya ta sake cewa "Ki bude Daughter ni ce" wasu sabbin hawaye ne suka cika idonta da ya tashi don kuka, ta fara kalle kallen bayin ta dau towel ta daura, Hajiya tace "Samha..." Cikin sanyin Murya tace "Toh Ummi" daga haka ta bude kofar amma ta kasa kallon Mami, Hajiya tace "Haba samha sai ki kwana a bayi?" Ita dai bata ce komai ba, Hajiyar da tausayinta ya rufeta sosai tace "Dau kayan ki ki sa kin ji" bbu musu Samha ta dau dogon rigar ta ta saka, Mami ta mika mata Hijab shi ma tasa, snn ta kama hannunta suka fita, har lkcn yana xaune balcony, suna fitowa ta yi ido hudu da shi, ta dauke idonta da sauri, shi kam kasa daina kallonta yyi, wani mugun sonta na fizgarsa ga tausayinta, Mami bata ko kallesa ba tana rike da ita suka fita balcony din tayi part dinta da ita. Suna shiga parlorn Hajiya Fatima ta bi su da ido don tana xaune parlon, Ita dai Samha bata dago kai ba har Hajiya ta shiga da ita bedroom dinta, tana kallonta tace "Ki shiga kiyi wanka xaki ga sabon toothbrush a bayin ma kin ji" kai Samha ta gyada mata ta nufi bathroom din, bayan minti sha biyar ta fito taga kayanta ajiye bakin gadon da mai da turare, duk a sanyaye ta gama shiryawa ta xauna nan kasan dakin, hawaye ya shiga sakko mata, ta rasa takamaiman abinda ke ranta a lkcn, she know she's regretting following Aliyu, ta fashe da kuka sosai tana tuna furucin mum dinta always na cewa musulmai ae bbu abinda suka iya sai cin amana, does this mean her mum is right, she never expect such from Aliyu, bude kofar dakin aka yi, ta sunkuyar da kanta tana share hawayen idonta, Ummi ta karaso dakin tana kallonta tace "Kuka kuma Samha?" Tashi ki xauna kan gado, Samha ta kasa dagowa har sai da Ummi ta kuma yi mata magana, ta mike jiki ba kwari ta xauna gefen gadon, Ummi tace "Bana son in kara ganin kina kuka, ko baki dauke ni matsayin uwa ba Samha" girgixa kai kawai tayi, Ummi tace "Toh ki daina kukan nan, kar ki wani damu kanki kuma ki saki jikin ki a nan kamar kina gidan ku kin ji" kai kawai ta gyada bata iya ta bude baki ba, Ummi ta fita ba a dau lkci ba ta dawo mata da breakfast ta ajiye mata tace "Sakko ki karya" ba musu Samha ta sakko kasa, Ummi ta juya ta fita, da kyar Samha ke shan tea din duk damuwa yyi mata yawa, yanxu ae in ta koma gida kilan sai dai wata kuma ba ita ba tasan Mumy will never take it likely with her, or kawai ta wuce kaduna gun aunt dinta, abinda xuciyarta ke raya mata knn kuma taji ta gamsu da hakan, khadija ce ta shigo dakin ta wara ido tace "Ashe kina nan Sis Samha, Ummi tace baki da lafiya, ya jikin?" Murmushi Samha ta kirkira tace "Da sauki...." Khadija ta xauna dakin tace "Ayya, Allah ya sauwake" khadija na fita Samha ta mike ta shiga gyaran Bedroom din duk da bbu wani gyaran da yake bukata, snn ta kwashe plate da cup din da ta karya ta fita da su, Har lkcn fatima na xaune parlor idonta a kan wayar hannunta, tana dago kai suka hada ido da Samha, Samha ta dauke kai ta nufi kitchen, Fatima ta bi ta da ido, tana ajiye kwanukan hannunta ta fito parlor, Dai dai nn Hajiya ta shigo tana kallon Samha tace "Har kin karya?" Kai kawai Samha ta gyada mata, Hajiya tace "Toh mu je daki" bin bayanta Samha tayi suka koma dakin, Hajiya tace "Kiyi xaman ki a nan...." Har yamma Samha na bedroom tare da Khadija dake ta bata labarai, sae dai idan lkcn sllh yayi su tashi su yi, Ummi kuwa tun Sha daya ta fita gun aiki, Samha tayi iya kokarinta na ganin Khadija bata gano tana da damuwa ba don sae biye mata take, sai dai taji haushin kin barin ta ita kadai da Khadijar tayi don her plan was to leave, ko kara ganin Aliyu bata son yi, Fatima ma na gidan throughout sae dai bata ko leka inda suke ba, karfe biyar Khadija tace "Sis Samha mu je ki raka ni kitchen in daura dinner mai aikinmu bata xo ba yau, Sis fatima kuma is still pretending she is not okay" murmushi Samha tayi ta mike ta bi bayanta suka wuce kitchen, Shinkafa Khadija ta daura, Samha kuma ta dau kayan miya tana wankewa, can ta kalli Khadija tace "Rabi'a bata nan ne?" Khadija tace "Tana gidan wani uncle din Ummi tun jiya" Samha bata kuma cewa komai ba, har ta gama gyara kayan miyan, Khadija tace "Yauwa ya ma name din spice din nn da kika sa ranan a stew mai kamshi?" Yar dariya Samha tayi tace "Xaki sa ne ke ma?" Khadija tace "Ehh mana don Ummi tasan nice nayi girkin yau ba sis Fatima ba" Samha tace "Toh bari in dauko maki" Har ta isa bakin kofa sai kuma tayi jim, ta gefen ido ta lura khadija na kallonta kawai sai ta fita, jiki a sanyaye ta nufi nasu part din, ta shiga kitchen da sauri ta dauko spices din gaba daya ta fito dai dai bakin kofar fita ta kusa cin karo da shi, ta koma baya a tsorace, shi kam kallonta kawai yake can yace "Am, am sorry Samha forgive me pls" hade rai tayi ta bi gefensa xata fita ya rikota ta fasa ihu, muryar Ummi suka ji tana cewa "Are you stupid Aliyu, sake ta immediately..." Saketa yyi ta bi ta gefensa da sauri ta fice, Ummi tace "What brought you here?" Abun hannunta ta nuna mata, Ummi tace "Bana son in sake ganin ki part din nn...." Samha bata ce komai ba ta bar wajen, Ummi na masa wani irin kallo ta jefa masa envelope da makullin motar dake hannunta ta bi bayan Samha, lumshe ido yayi kafin ya bude har sun shiga part din Hajiya, duk jikinsa yyi sanyi wani hukunci knn Ummi ke son dauka? Da kyar ya duka ya dau files din da makullin mota ya juya ya fita daga compound din. Karfe takwas yana kwance parlor kiran Ummi ya shigo wayarsa yana dauka tace "Ka taho ka karbi abinci" toh kawai yace ta kashe wayarta ya mike xaune, can dai ya tashi ya fita, Fatima na xaune balcony textbook gabanta alamar karatu take, bai ko kalleta ba ya isa bakin kofa ya kwankwasa, ajiye pen din hannunta tayi tana naxarin what's d meaning of Samha staying a part dinsu tun sassafe, tana son gano me ke faruwa amma tasan Ummi will never tell her, Khadija ce ta bude kofar ya shiga, Ummi na parlon da Samha da Khadija, Samha ta sauke idonta kasa, shi kam idonsa na kanta ya xauna, Ummi tace "Ga abincin ka a dinning...." Karasawa yyi ya dauka ya dawo yace ya gode, Ummi tace "Godiya kuma, Pls gobe da safe kafin ka fita gun aiki xaka je dauko Yusuf a airport boy, though am nt sure ko goben xae taho, in goben ne i will give you a call" Abuturrab yace "Toh Mami..." Daga haka ya kuma kallon Samha da ta dago ita ma don satan kallonsa, suna hada ido tayi saurin dauke nata idon. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 42..... Kasa daurewa Fatima tayi misalin karfe tara Samha na daki tare da Khadija ta shiga bedroom din Ummi, xaune ta tadda Ummi idonta sanye da glass tana aiki gaban computer, ta karasa ta xauna tace "Ummi..." Ummi ta juya tana kallonta tace "Ya aka yi?" Tace "Uhm wai da gaske gobe yaya Yusuf din xai iso?" Ummi ta ci gaba da abinda take tace "Ki kirasa ki ji mana" Shiru tayi bata ce komai ba don ba tambayar da ya kawo ta knn ba, Can dai tayi karfin halin cewa "Ummi me Samha take yi a nn ne wai?" Juyawa Ummi ta kuma yi ta kalleta tace "How is her staying here affecting you?" Yake tayi tace "Noo, Ummi it's surprising ne ta bar mijinta ta xo nan, i tot bata da lafiya ne ma" Ummi tace "Toh ba matsalar ki ba ne..." Daga haka Ummi ta ci gaba da abinda take, Fatima ta mike ta fita daga dakin cike da jin haushin abinda ummi tayi mata. Dakin yayanta ta shige tayi kwanciyarta. Da asuba Ummi ta shigo tada khadija tayi sllh, ga mamakinta sai taga sun ma tashi suna sllhn, tsaye tayi bakin kofa tana kallon Samha, a xuciyarta tace "Ikon Allah, amma wnn ai aikin baban giwa take..." Tausayinta sosai taji a ranta ta kuma dau kudirin xata dau time ta tambayeta her view about islam, is she interested, but ga dukkan alamu ma she is interested tunda har ta iya tashi da asuba tayi sllh, juyawa Ummi tayi ta fita. Abuturrab na idar da sllh part din Ummi ya taho don jin ko xae je airport din kuma, "Na kira wayarsa bai je ba, je kayi abinda xaka yi idan ma ya iso sai ya dau taxi kawai" cewar Ummi kenan bayan ta fito, yace "Toh Mami" daga haka ya juya ya bar wajen. Xama Abuturrab yyi a parlor ya rike kai bayan ya koma part dinsa, he never taught hukuncin da Ummi xata dauka kenan, me yasa take kkrin nisanta shi da Samha, sae yaji duk xaman gomben ma ya ishesa, damuwa yyi masa yawa, what happened the day before yesterday was just a mistake, sharrin shaidan. Ya rasa gane whether he is regretting telling her or not, gaba daya yaji bai jin xai ma iya ci gaba da xama garin. Samha na xaune daki tana kallon khadija dake karatun qur'ani sai dai gaba daya hankalinta bai gun, gaba daya tunaninta na gun Abuturrab is she missing him or what, hawaye taji na neman taruwa idonta, why is all this happening to her in just 2 month, kwanciya tayi a hankali ta juya kanta hawaye na sakko mata. A ranan Abuturrab na xaune office ya jinginar da kansa jikin kujera wayarsa dake gabansa ya fara ring, dauka yayi yaga Hajiya Mariya ce ke kiransa, ya lumshe ido ya daga kiran ya kai kunne, cikin sanyin murya yyi mata sallama ta amsa daga daya bangaren, ya gaisheta tace "Abuu ko kira baxaka dinga yi ba, ya kuke?" Yace "Lafiya lau mum, ya gida?" Tace "Alhmdllh, ina Samhar?" Yace "Tana gida mum" tace "Kai kana ina?" Yace "Ina gun aiki Mum" tace "Aiki kuma, da wani qualification din" yayi murmushi yace "Uhn da na kai na Mumy..." Tace "Toh a ina ka samu aikin..." Bayanin Hajiya Hajarah ya shiga yi mata, Hajiya Mariya tace "Allah sarki, Allah ya mata albarka... Yanxu kuma Abuu haka xaka ci gaba da rayuwa da wacce ba muharramar ka ba..." Yace "Mumy i told Hajiya everything jiya da safe, shine ta dauki Samhar ta komar da ita nata bangaren i really can't tell what she is up to...." Hajiya Mariya tace "Maa sha Allah naji dadin hakan gaskiya, am happy akwai babba tare da ku da xata dinga gaya maku gaskiya tana nuna maku, what she did is the right thing...." Abuturrab yace "But Mum, kar ta raba ni da ita wlh mum baki ji yanda naji da ta mayar da ita bangaren ta ba..." Hajiya Mariya tace "Keep quiet, hakan shine dai dai, ta burge ni wllh... Idan ma conversion din ne gwara ita tayi converting dinta" kasa ce mata komai Abuturrab yayi, tace "Yea, sai mun yi waya" daga haka ta katse wayar ya ajiye ya rike kansa. Samha na kitchen tare da khadija da mai aikinsu misalin karfe biyar saura suka ji fatima dake parlor da wata Billy, wanda da alamar ita ta kirata ta xo tana cewa "Welcome big bro..." Khadija ta ajiye yankan salad din da take yi da sauri ta fice daga kitchen din tana cewa "Oyoyo yayana" tsaye Samha tayi bakin kofa tana kallon yayan nasu dake kkrin cire takalmin kafarsa ganin kanwartasa ya mike ya wara ido ya rungumeta yace "Oyoyo lil sis..." Kankamesa khadija tayi tace "I missed you broo..." Yace "I missed you too, ina Ummina" khadija tace "Bata dawo ba..." Yace "Rabi'a fah?" Tace "Tana gidan Abbu..." Sau daya ya kalli Samha da tayi saurin sunkuyar da kai ya amsa gaisuwar Billy ya wuce bedroom dinsa. Bayan Magrib Samha na kwance daki khadija ta shigo tace "Sis Samha ki fito mu ci abinci..." Samha ta kalleta tace "Ae daxu na ci abinci..." Khadija tace "Dinner fa ba lunch ba" murmushi Samha tayi tace "Toh ni dai na koshi...." Khadija tace "Ummi fa ce tace in kira ki" mikewa Samha tayi ta bi bayanta suka fito parlor, Dai dai lkcn da Abuturrab ya shigo parlorn, kanta a sunkuye ta karaso parlon, shi kam idonsa na kanta har ya shigo, khadija ta gaishesa ya amsa har lkcn idonsa na kan Samha, Fatima kuma idonta na kansa kamar xata cinye sa, ya xauna yace "Ga ni Mami..." Ummi tace "Abinci xaka ci dama, Samha kun gaisa kuwa?" Sai a snn ta dago kai ta kallesa, sai kasa daina kallonsa tayi, can tayi karfin halin cewa "Ina yini..." Ya kasa amsawa, Ummi tace "Ba ku ma gaisa da Yusuf ba Boy" daga haka ta kwalo ma Yusuf kira, Khadija tace "Ae bai shigo daga masallaci ba..." Bata rufe baki ba Yusuf ya shigo parlon da sallama, Abuturrab ya juya ya kallesa, karasowa yyi parlon yace "Ummi am jet hungry...". Ummi tace "Ga abinci can dinning ai, bayan tafiyar ka Allah ya hada ni da wani son wanda ya take ka a rashin ji ma, ka gansa yana nn yana ban wahala shi ma..." Sosai ta ba Abuturrab dariya, khadija ta fashe da dariya ita ma, Samha kam murmushi tayi ta sunkuyar da kai, Yusuf ya wara ido yana kallon Abuturrab yace "Really Ummi..." Daga haka ya mika masa hannu murmushi dauke fuskarsa suka gaisa yace "I am barrister Yusuf Ahmad...." Abuturrab ya mayar masa da murmushin yace "I am Dr Aliyu Ahmad...." Yusuf yace "It's nyc meeting you..." Kai Abuturrab ya gyada masa har lkcn murmushi fuskarsa yace "Same..." Ummi na kallon Samha tace "Kun gaisa da shi dota?" Sai a snn Samha ta kallesa shima ya juya yana kallonta, a hankali tace "Ina yini?" *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 43..... Yusuf da ke kallonta shi ma yace "Lafiya lau...." Daga haka Ummi ta mike tace "Ga dinner can a dinning, fatima u serve it..." Mikewa Abuturrab ma yyi yace "Mami na taho da abinci fahh" kallonsa Ummi tayi tace "Toh ae bn ce ka taho da abinci ba, ga abinci can nace a dinning" Daga haka ta nufi dinning din ganin Fatima bata da niyyar mikewa, da kanta tayi ma kowa serving abincin ta juya tana kallonsu, Yusuf ne ya fara nufar dinning din fatima ta bi bayansa, ya ja kujera ya xauna, Khadija ta kalli Samha tace "Mu je..." Mikewa Samha tayi ta bi bayanta suka tafi, Khadija ta ja mata kujerar da ke kallon na Yusuf, ta xauna, snn ta xauna gefenta, Ummi na kallon Abuturrab da ya ki tahowa tace "Toh ko sai na dauko ka..." Murmushi yayi ya taho dinning din ba don ya so ba, ya ja kujerar dake gefen na Fatima a hankali ya xauna, can ya kalli Ummi yace "Ke baxa ki ci ba Mami..." Ummi tace "A'a ku dai ku ci My boy..." Daga haka ta wuce daki, Yusuf kam kansa na kasa yana cin abincin gabansa sai dai lkci lkci ya kan dago ya kalli Samha dake opposite dinsa, wanda hakan yasa duk ta takura ta kasa cin abincin, Abuturrab ya dago ya kalleta, ganin ba dagowa xata yi ba yasa ya sunkuyar da kai ya shiga cin abincin gabansa, fatima kuma sai satan kallonsa take, Kamar ance Abuturrab ya kalli Yusuf ya ga idonsa a kan Samha, ji yayi abincin na neman dawo masa ya mike da sauri hade da rufe baki kamar me shirin amai, Fatima ta mike ita ma da sauri tana kallonsa, Yusuf ya tashi shi ma da mamaki yace "What happened...." Abuturrab na girgixa kai yace "Am... Am not okay, i need to throw up...." Daga haka ya juya da sauri ya bar dining din, Samha ta bi sa da ido, ae bata san lkcn da ta mike ta bi bayansa ba, Yusuf ya bi su da ido, can ya kalli Khadija yace "Who's she?" Khadija tace "His wife..." Shiru yyi yana kallonta ko kiftawa bbu, Samha na fita taga har ya kusa balcony, ta bi bayansa da sauri, nan bakin kofa ta gansa durkushe sai kkrin amai yake ya kasa, ji yyi gaba daya cikinsa ya hautsine amma ya kasa amai, ga wani mugun bugu da xuciyarsa ke yi, ta durkusa gabansa ta rikosa hankali tashe tace "Me ya faru doctor, baka son abincin ne, ni da khadija fa muka yi..." Bai iya ya ce komai ba, jin hannunsa a shoulder dinsa yasa shi fara jin saukin abinda yake ji, ganin ya fara nutsuwa yasa tayi shiru tana kallonsa, a hankali ya dago idonsa da yayi jajir yana kallonta, sauke idonta kasa tayi, sai ji tayi ya rungumeta, tayi lamo jikinsa tana jin bugun xuciyarsa, duk yanda ya so bude baki yayi mata magana kasawa yayi, lkci daya hawaye ya kawo idonsa, ta dago a hankali ganin haka sai ta fashe da kuka, cikin sanyin murya yace "I love you Samha, i will be nothing without you... Kar ki bari son ki ya xama ajalina, don't make me a living dead...." Ta rungumesa cikin kuka tace "Why is all this happening to us... Why did you teach me how to love you deep...." Saketa yyi ya goge fuskarsa jin motsi a balcony ya mike tsaye sai ga Ummi ta shigo, wani kallo take masa daga sama har kasa strictly tace "What happened?" Rasa abinda xai ce mata yyi, tace "Baka ji na ne boy?" Da kyar yace "Mami... Ji nayi i want to throw up...." Kallon Samha da ta tashi tsaye ita ma tayi ta hade rai tace "Me kika xo yi nan?" Kamr xata yi kuka tace "Ummi, naga..." Kofa Ummi ta nuna mata tace "This shud be ur last, kada ko da wasa ki sake shigowa nn, leave now" A hankali tace "Toh Ummi..." Daga haka ta fita, Ummi ta kallesa tace "If you like throw up till tomorrow...." Daga haka ta juya tayi ficewarta, ya jingina jikin bango xuciyarsa na bugawa. Samha na komawa bata yarda ta je dinning ba tayi shigewarta dakinsu Khadija ta kwanta duk jikinta yyi sanyi, har ta fara bacci Khadija ta tada ta wai ta tashi tayi Isha, mikewa tayi ta shiga bayi. Karfe goma Yusuf ya shiga bedroom din Umminsa, as usual tana aiki, ya xauna tace "Ya aka yi Barrister..." Ya shafa kai yace "Gobe Abba xai taho week end ko Ummi?" Ta girgixa kai tace "Sai next week" yace "Okay, Ummi wai Aliyu ashe matarsa ce yarinyar nn" Ummi ta kallesa tace "Wa ya gaya maka?" Yace "Khadija..." Ta girgixa kai tace "Ba matarsa bace...." Lumshe ido yyi na kusan second biyar kafin ya bude a hankali, shiru Ummi tayi kamar bata so fadin hakan ba, duk yusuf na lura da ita, can tace "Amma ba wai nace kaje ka fada masu bane, i mean ur siblings, shi kuma you don't say anything to him about it... Yanxu ka tashi kaje can part din nasa sai ku kwana tare" da sauri yace "Why???" Ta kallesa tace "Sbda ina son ku yi xumunci sosai, he is very good nd brave..." Yace "A ina ma kika samo sa Ummi?" Tace "You leave now, sai da safe... You've interrupted me enough...." Murmushi yayi ya mike yace "Aiit Mother, sai da safe... But in ji dai bai da ji da kai, idan naga haka xan dawo inyi kwanciyata a nan" murmushi tayi tace "No, he is nyc son" sai da safe Yusuf yyi mata ya fita, a parlor ya kusa cin karo da Samha da taje dauko ruwa kitchen ta koma baya da sauri, ya koma gefe yace "Yi wucewar ki..." Gefensa ta bi ta wuce kanta a kasa, shi kuma ya nufi kofa da system dinsa xuwa part din Abuturrab, kwance ya samesa parlor Abuturrab ya mike xaune ganinsa, Yusuf yace "Hi Dr, came to spend d nyt here, hope m welcome..." Murmushin karfin hali Abuturrab yayi yace "Of course you are Brrstr..." Yusuf yace "Ohh tnx..." Daga haka ya xauna gefen Abuturrab yana kkrin kunna system dinsa yace "As I've said before, i am yusuf, born nd brought up in Abuja... I school in Uk, i soo love football" daga haka ya kalli Abuturrab dake kallonsa, Abuturrab yace "Uhn! That's nyc... I was born nd breed in kano, studied Medicine nd Surgery in Uk, amm may be i do love table tennis, and.... Snooker" dariya yusuf yyi ya kai masa Knuckle, Abuturrab ya dunkule hannunsa yana murmushi ya kai kan nasa, Yusuf yace "It's nyc meeting you...." *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By Khaleesat Haiydar📚✍🏻 44..... Abuturrab ne ya fara mikewa bayan awa daya yana kallon Yusuf yace "If you er done sai ka shigo ni xan kwanta yanxu" Yusuf yace "Aiit...." Daga haka Abuturrab ya shiga daki yayi kwanciyarsa sai dai ya kasa bacci, ya rasa me ke masa dadi a duniyar, har Yusuf ya shigo bayan kusan minti talatin bai yi bacci ba, sae dai idonsa a lumshe suke, Yusuf ya shiga toilet ya dauro alwala snn ya fito yayi kwanciyarsa. Da asuba kusan a tare suka tashi duk suka yi alwala suka fita xuwa masallaci, ko da suka dawo yusuf ya koma yayi kwanciyarsa shi kuma Abuturrab ya shiga bathroom. Kafin karfe bakwai har ya gama shirinsa, bai tada yusuf dake bacci ba ya dau makullin motar dake gun sa ya fita, yana warming motar yaji an kwankwasa masa glass ya daga kai ya ga fatima ce tsaye, ya dauke kai snn ya sauke glass din, ba tare da ya kalleta ba ya shiga jiran jin abinda xata ce, a takaice tace "Good morning" har lkcn bai kalleta ba yace "Morning how you?" Tace "Ummi tace in kira ka" yace "Ohk..." Juyawa tayi ta bar wajen, sai a snn ya daga kai ya bi ta da kallo, can ya bude motar ya fita ya nufi part din Hajiya, yana shiga parlon ya xauna, Ummi ta fito daga kitchen ya sauke kai kasa ya gaida ta ta amsa tace "Baxa kayi break ba boy?" Yace "Xan yi a office..." Tace "A'a ka jira dai kayi kafin ka tafi ka ji... Me ya same ka jiya wai?" Daga kai yayi ya kalleta yace "Ba komai Mami, am ohk now..." Kallonsa kawai take bata ce komai ba, can dai tace "Shknn ka je khadija xata kawo maka kayan karin, naga kamar baka son cin abinci a nn koh?" Murmushi yayi ya mike yace "Toh nagode Mami" daga haka ya mike ya fita, karasawa yayi ya kashe motar snn ya shiga parlonsa ya xauna, bayan kusan minti bakwai aka bude kofar, daga kai yayi yaga fatima ce ta shigo rike da tray na breakfast, ya kauda kai har ta karaso ta durkusa gabansa ta ajiye tray din, ta dau cup xata bude flask ya dakatar da ita yace "No.. No kiyi tafiyar ki...." Bata tanka sa ba ta bude flask din xata xuba ruwan shayi a cup din, yace "Wai ba kya ji ne, i said..." Dago kai tayi tayi masa wani kallo ta xuba ruwan a cup snn ta rufe flask din ta shiga hada tea'n, mamaki ne ya cika sa, tana gama hadawa, ta ajiye gabansa ta bude plate din dake dauke da Irish da kwai sai plantain, snn ta mike tayi ficewarta ya bi ta da ido, can yayi tsaki ya dau tea din. Damuwa bai barsa ya ci break din da yawa ba kawai ya mike daga karshe ya fita ya hau mota ya fice xuwa office. Khadija da Samha na shirin tafiya islamiyya Ummi ta shigo dakin, tana kallon Samha tace "Ki bari gobe ki je Samha... Ita khadija ta yi wucewarta" Samha tace "Toh" Khadija ta turo baki tace "Sbda me Ummi.... Yau fa kika ce xata fara" Ummi bata tanka ta ba ta fita, haka khadija ta gama shirinta ta wuce ita kadai ba don ta so ba, Samha kam tayi kwanciyarta don dama duk sai taji ma xuwa islamiyyan ya fita kanta... Tana kwance ita kadai dakin aka bude kofa ta kalli Kofar, Yusuf ne tsaye wajen ganin ita kadai ce dakin bai karaso ba yana kallonta yace "Good morning" ta mike xaune tace "Ina kwana..." Ya d'an yi murmushi yace "Kin tashi lfya?" Sunkuyar da kai tayi ya juya ya fita ta koma ta kwanta, mai aiki ce ta shigo tace mata Ummi na kiranta, ta dau hijab dinta ta sa ta fita xuwa bedroom din Ummi, xaune ta ganta gaban computer, ta xauna kasa tace "Ga ni Ummi..." Ummi ta kalleta tace "Tashi kiyi xaman ki sama..." Ba musu ta mike ta koma gefen gado, Ummi tace "Samha..." A hankali ta dago tana kallonta tace "Na'am" Ummi tace "Duk tambayar da xan maki ki fada min gaskiya, kar ki ji shakkan komai kin ji daughter...." Samha ta gyada mata kai, Ummi tace "Do you have interest for islam?" Kallonta kawai Samha take bata ce komai ba, Ummi tace "Talk to me dear..." Hawaye ne ya cika idonta, a hankali ta girgixa kanta alamar A'a, shiru Ummi tayi tana kallonta, can tace "Baki da interest knn?" Samha ta gyada mata kai, Ummi tace "Toh me yasa kika yarda kika biyo Aliyu" hawaye sosai take yi, ta kasa cewa komai, cikin sanyayyan murya tace "You take me as ur mother Samha, tell me what's in ur mind kar ki ji komai...." Samha ta shiga goge fuskarta bata ce komai ba, Ummi tace "Tell me why did u follow him bayan baki da ra'ayin addinin islam..." Murya can kasa tace "I don't know... Buh i know i love him shi yasa na biyosa, snn ya taba ce min in yi addinina yayi na sa...." Da mamaki Ummi ke kallonta, can tace "Toh me yasa kike sllh, har kike sha'awar shiga islamiyya, kuma wa ya koya maki sllhn?" Wasu sabbin hawayen suka kawo idonta cikin rawan murya tace "Aunt dina dake kaduna musulma ce ita ta koya min sllh, she is my dad's younger sister...." Ummi tace "Toh islamiyyan da kike son shiga fa?" Shiru tayi bata ce komai.... Ummi tace "Talk daughter" ta share idonta a hankali tace "Kawai dai ina son xuwa ne...." Ummi tace "Toh kince you don't have interest for islam me yasa kika yarda da musulmi kika amince masa har kika biyosa kin san baki son musulinci?" Kuka ta shiga yi a hankali, Ummi tace "Kuka kuma? Ni ban ce ki min kuka ba Samha...." Bude kofar dakin aka yi Yusuf ya shigo da sallama... Kallonsa Ummi take, shi ko idonsa na kan Samha barin da yaga hawaye idonta, Ummi tace "Ya aka yi Yusuf?" Kallon mum din tasa yayi snn ya kalli Samha, da harshen fillanci yace "Ummi kukan me take yi? Me ya faru?" Sharesa Ummi tayi ta kunna computern gabanta, Samha kam bata dago kanta ba, can Ummi ta kallesa da yaren ita ma tace "You leave now...." Da damuwa yace "But Mum she is crying...." Hade rai Ummi tayi hakan yasa ya juya ya fita kawai, Ummi ta kalleta ganin kukan gaba yake karawa cikin sanyin murya tace "Tashi ki je Samha we'll talk later" kamar jira take ta mike da sauri don da alama bata son xancen ta fita daga dakin Ummi ta bi ta da kallo cike da tausayinta. Daki ta koma tayi kwanciyarta, tayi kukanta me isarta snn bacci ya dauketa. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By Khaleesat Haiydar📚✍🏻 45..... Sai bayan Khadija ta dawo daga islamiyya Ummi ta wuce clinic don bata son barin Samha ita kadai, karfe uku saura Abuturrab na xaune office yana attending ma patient kiran Ummi ya shigo wayarsa, dauka yyi ya kai kunne hade da yi mata sallama, Ummi ta amsa tace "Kana office boy?" Abuturrab yace "Ehh Mami..." Tace "Toh ina jiran ka" daga haka ta katse wayar, yana sallaman patient din ya mike ya fita xuwa office dinta, sai da tayi masa izinin shigowa bayan ya kwankwaso kofar snn ya shiga da sallama, kallonsa take ganin yanda ya rame sai taji tausayinsa ba kadan ba, ya karaso kansa a kasa ya xauna kujera yace "Gani Mami" ajiyar xuciya ta sauke tana kallonsa har lkcn tace "You will think i'm mean ko boy, ko daya wllh am only trying to put u on d right way ne, kaga yarinyar nn ba muharramar ka bace, it's nt decent it's nt proper ku xauna roof daya da ita... Kasan da haka kuma, ni ban ga laifin ku ba Aliyu, nasan soyayya gaskiya ce amma tunda har ka buda min cikin ka i can't continue watching u disobey Allah, ina son ka tamkar d'an da na haifa a cikina right frm d time i saw u... Yanxu kai ka gaya min me xuciyar ka ke raya maka a kan yarinyar nan... What's d next step u wanted taking kafin abinda ya faru ranan da daddare" bai iya ya dago kansa ba cikin sanyin murya yace "Mami ni bani da niyyar cutar ta aurenta nake son yi...." Ummi tace "Aure? Ta ya amma" ya langwabar da kai yace "Kin ga idan na aureta conversion dinta xuwa islam baxai dau lkci ba..." Murmushi Ummi tayi tana girgixa kai tace "Na xaunar da ita mun yi magana daxu kasan abinda tace min?" Girgixa kai yayi, Ummi ta ci gaba "She said she don't have interest for islam boy, haka tace min, na kuma yi mamakin jin hakan" Da sauri Abuturrab yace "Noo Mami, she's just confuse ne wllh, buh wanda bai da interest ae baxai dinga sllh ba, kinsan Mami tun da dadewa fa na rabata da duk wani abu da xai dinga kusantarta da Christianity, kuma duk ta hakura ta bari" Ummi tace "That's because she love's you, soyayya yasa ta biye maka boy" yace "No Mami baya ga soyayya ma idan mutum har xuciya yake abun sa ai bbu abinda ya isa raba sa da shi.. Her dad was a muslim then fa, kakanta ma Musulmi ne har ya rasu, kawai mahaifinta bai da rabo ne, amma in shaa Allah shi ma xai dawo hanya madaidaiciya, uwar ta kam dama ba a magana tayi nisa sosai" Ummi dake ta kallonsa ta gyada kai cike da gamsuwa tace "Haka ne boy, na kuma lura abinda yasa ta fara loosing interest sbda nisanta ku da juna da nayi ne, buh i have no other alternative kada in xamo uwar banxa, abinda baxan bar d'a na yayi ba to d'an wani ma baxan bari yayi ba.... Kuma xancen xaka aureta ynxu bai taso ba boy, ka bari sai ta amshi islam don kanta ba don auren ka ba... Xaka aureta amma not so soon, ynxu dai ka dinga yawan shigowa a kai a kai ta daina jin kadai cin da take ji, komawanta can ne dai baxae taba yiwuwa ba, kai da Yusuf kuyi xaman ku a can tunda xai jima sosai a nan, one more thing boy pls pls ka daure kaje gida ko don mahaifiyar ka..." Kallonta yayi da sauri yace "Sai ince Samha tana ina, baxa ki gane ba Mami ai ina kai kaina gida yanxu ni nasan kano yayi ma Abbana kadan yyi min hukunci sae dai Abuja, xan je gida amma ba yanxu ba" kallonsa kawai Ummi take, can ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh shknn boy, kai ma ka rage ma kanka damuwa bana son kana raman nn, Samha dai ba rabaka nayi da ita ba, duk lkcn da kake son ganinta sai ka shiga har hira ma kuyi, i won't stop that" ya d'an yi shiru sai kuma yace "Toh Mami nagode, amma plss let this continue to be a secret btwn us bana son a san she's nt my wife" da damuwa ya kare maganar, Ummi ta gyada kai tace "Alryt boy" a hankali cikin sanyin murya yace "Mami... mami ko yusuf ma fa kar ki ce masa ba matata bace...." Shiru Ummi tayi tana kallonsa, Gabansa ne ya fadi sosai ganin kallon da take masa, sai kuma tayi saurin gyada kai tana murmushi tace "Aiit, u can leave now boy.... I will let no one know" Mikewa yayi ya mata sallama ya fita, for the 1st time tun bayan faruwan incident din ranan yaji hankalinsa ya kwanta sosai. Fatima ce xauna balcony da kawayenta biyu handouts a gabansu Khadija da Samha suka fito, Khadija tace "Sister xa mu je siyo airtime..." Fatima tace "Ohk" Bin su da kallo fatima tayi suna yin nisa billy tace "Kin ki gaya min dalilin dawowar yarinyar nn part din ku..." Fatima tace "How many times do i have to tell you nima ban sani ba kuma ban san ta yanda xan sani ba Billy, I've snooped, I've put an eye all to no avail.. Ummi ba gaya min xata yi ba, that silly khadijah of a being ma ko da tasan abu she won't tell me" farida tace "Buh guy din ya fara sake maki kuwa?" Fatima bata ce komai ba ta dau handout din gabanta, Billy tace "i have a plan for you teemah..." Yusuf na xaune karkashin artificial tree dake compound din gidan yana waya amma idonsa da hankalinsa na kan Samha da khadijah dake tahowa, Samha ta saci kallonsa suka hada ido ta dauke nata da sauri, khadija tace "Yaya xa mu je siyo card..." Yace "Card?" Tace "Eh, airtime" yace "Ohk, taho in maki transfer" Tace "Toh yayana thank you..." Daga haka ta kama hannun samha suka nufi inda yake, kujera ta ja ta xauna tana kallon Samha ta dauko mata wani kujerar tace "Sit" Samha ta kirkiri murmushi ta girgixa kai tace "Thank you" Yusuf dake kallonta yace "Why?" Bata ce komai ba kuma bata kallesa ba, yace "Ki xauna" bbu yanda ta iya haka ta xauna kan kujerar, yana danna waya yace "1000 ya maki yawa koh?" Ta xaro ido tace "Noo yaya, ya isa fah" yayi murmushi yace "Tohm! Waec bai fito ba har ynxu koh" tace "Ehh muna ta jira..." Samha dai kallonsa kawai take, height dinsu xae xo daya da Abuturrab haka ma haskensu, tana kkrin tantance wanda ya fi kyau cikinsu ya dago kai ya ga tana kallonsa, mikewa tayi da sauri tana kallon khadija tace "Amm, xan... bari in shiga ciki in taya usaina..." Daga haka ta bar wajen kmr warce aka kora ya bi ta da ido yana murmushi, Khadija tayi tagumi tana kallonsa, can dai tace "Big bro.... She's someone's else property fah?" Kallonta yayi da sauri yace "Whose?" Ta hade rai tace "Ba na gaya maka ba Dr Aliyun nn mana...." Yusuf yace "Hmm yeah... Amma yaushe suka xo gidan nan?" Khadija tace "Xa su kusa 5 weeks fa" yace "Ohk, but why is she staying a part dinmu?" Ta bude ido tace "Nima ban sani ba wllh, at 1st nayi tunanin ko bata da lafiya ne ma" yace "Ohk, a ina Aliyun yake aiki?" Khadija tace "A clinic din Ummi..." Kallonta kawai yake can yace "Ohk, da suka xo garin nn baya aiki ne?" Khadija tace "Toh, nima dai bn sani ba amma Ummi dae ta basa aiki a clinic" Yusuf na gyada kai yace "Ohkk, daga wani gari suke?" Tace "Kano wai..." Yace "Ohk, amma bata gaya maki komai a kan ita da Aliyun ba, i mean ko a hira bata gaya maki san da suka yi auren ba...." Khadija da ta fara isa da tambayoyin tace "A'a ni fa ban taba tambayarta komai ba" Yace "Ohk, but is dis their 1st time in Gombe?" Mikewa khadija tayi don tasan in ta ci gaba da basa amsa sae su kai dare a gun, ta turo baki tace "Kai yaya, sai kace ka samu case.... Wnn ko a court sai haka ae ta ya ni xan yi in san ko sun taba xuwa gombe, ni dai tnx for d airtime xan je mu ci gaba da girki..." Daga haka ta kara gaba ya bi ta da kallo yana murmushi. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 46.... Karfe shidda saura Abuturrab ya dawo daga gun aiki, yana gama parking ya fito yana kallon Yusuf dake compound din har lkcn, karasawa yyi ya basa hannu suka gaisa, Yusuf yace "Welcome back..." Abuturrab yace "Thank you, iska kke sha knn" Yusuf ya shafa kai yace "Not really am making a call...." Abuturrab yace "Aiit" daga haka ya wuce part dinsa, har aka kira Magrib Yusuf na xaune waje, sai da ya ga fitan Abuturrab masallaci snn ya tashi ya karasa tap din dake compound din yyi alwala ya bi bayansa. Kusan a tare suka shigo da Ummi compound din hakan yasa suka karasa can part din gaba daya don gaisheta, Abuturrab bai jima parlon ba ya koma part dinsa don tun da ya shiga bai ga Samha ba, yana kwance idonsa kan news da ake a tv aka bude kofa hade da sallama, Khadija ce ta shigo tare da Samha rike da abinci hannunta, har suka karaso inda yake idonsa na kan Samha, khadija ta ajiye abincin hannunta tace "Ina yini Uncle" ya kalleta ya amsa yace "Lafiya dija, sannu da aiki" tayi murmushi bata ce komai ba, Samha da kanta ke kasa tace "Ina yini?" Ya kalleta yace "Lafiya lau..." Sai a snn ta daga ido ta kallesa, murmushi tayi ganin yanda yake kallonta, tace "Ya aiki?" Yace "Alhmdllh...." Mikewa khadija tayi tace "Bari in dauko plate...." Daga haka ta wuce kitchen, saukowa kasa Abuturrab yyi yana kallonta har lkcn, cikin sanyin murya yace "Kin guje ni Heart beat...." Murmushi take ta girgixa kai tace "A'a" Dago kanta yyi ya kamo hannunta yana kallon kwayar idonta yace "I love you Samha...." Murya can kasa tace "I... i love you more" rungumeta yayi kan idon yusuf da ya shigo parlon a lkcn, Khadija kuma ta fito daga kitchen rike da plate, a hankali Samha ta xame jikinta, Yusuf kuma pretends he saw nothing yana danna waya, mikewa Samha tayi tana kallon Khadija da ta ajiye abun hannunta tace "Ba mu kai ma Ummi abinci ba" Daga haka ta nufi kofa Khadija ta bi bayanta. Ummi na xaune bedroom dinta Yusuf ya shigo, kallonsa take har ya nemi waje ya xauna, ta kalli agogo ganin goma ya wuce tace "Baka tafi can ba?" Yace "Yanxu xan wuce" Bata kuma cewa komai ba ta ci gaba da shan fruit din gabanta, Yana kallonta yace "Ummi...." Kallonsa tayi tace "Ya aka yi?" Ya shafa kai yace "Ummi ya Aliyu suke da yarinyar nn ne..." Wani kallo tayi masa tace "What's ur problem with that Yusuf, if am nt mistaken you've asked me that before, fine... Matar sa ce are you okay by that?" Yar dariya yyi yace "Buh few days ago ce min kika yi ba matarsa bace Ummi, how's this? Hmmm?" Hararansa tayi tace "Yea sun rabu ne then buh ynxu everything is normal" kallonta yake ko kiftawa bbu kmr me son gano abu, ta ci gaba da cin fruits dinta ba tare da ta kuma kallonsa ba, can ya dai yace "Toh mai take xama yi nan har yanxu?" Cike da masifa tace "Lemme rest pls Yusuf, i want him to know her value shi yasa har yanxu bata koma ba, kuma baxa ta koma ba..." Shiru yayi yana kallonta, can yace "Amma within dis short period din xamansu a gidan nn har kuka saba haka kika gano suna da prob... buh em fatima told me sabon aure ne, sabon aure shine har aka fara samun matsala, from my investigation na gano abu Ummi...." Mikewa tayi a fusace tace "Enough! Leave right away" mikewa yayi yana shafa kai fuskarsa dauke da murmushi ya nufi kofa ya fita, Ummi ta xauna hade da sauke ajiyar xuciya underneath her breathe tace "Damn it! Shi wai Barrister, Ya Allah kar ka bari ya gano komai kar in xama mara alkawari, i spoilt everything at d beginning" Yusuf na fita har xai nufi kofa yaji motsi kitchen a tunaninsa Khadija ne ya karasa kitchen din, Samha ya gani tana wanke wanke, suna hada ido ta dauke kai ta ci gaba da abinda take, shiga kitchen din yyi ya rufe kofa yace "Sannu da aiki" tace "Na gode" yana gyada kai yace "Ohk, ya ma sunan naki?" Ba tare da ta kallesa ba tace "Samha" yace "Nyc.... Ain't you missing home" da sauri ta kallesa sai dai bata ce komai ba, ya mata murmushi yace "You re nt tunda ga Aliyu koh" dauke kai tayi, dai dai nn aka bude kofar kitchen din, juyawa yyi da sauri, Ummi ta shigo, kallon Mamaki take masa tace "Me kke nn kuma Yusuf?" Yace "Ummi ruwa na xo sha, just came to take a glass of water...." Hade rai tayi sosai tana kallonsa, ya kalli Samha yace "Good nyt" a hankali tace "Thank you" daga haka yace ma Ummi ma sai da safe, ya fita ba tare da Ummi ta tanka sa ba. Ummi ta ajiye bowl din hannunta duk jikinta yyi sanyi ta juya ta fita. Ko kadan Abuturrab bai rintsa ba cikin dare, he was just planning on what to do next, yasan Ummi is truly good to him but bai jin xai iya ci gaba da xama garin when yusuf is around, May be some other time xai dawo gun ta don baxai taba mance irin halaccin nn da tayi masa ba, But he can't stay in gombe with his Samha any longer, kafin assalatu ya gama concluding next step din da xai dauka, and he was relieved. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By Khaleesat Haiydar📚✍🏻 47..... Washegari Yusuf na bacci Abuturrab ya gama shirinsa, atm cards dinsa kawai ya dauka snn ya fita tun bakwai da rabi bai yi ba, bai fita da mota ba don kar ma Ummi ta ji fitarsa, clinic ya tafi, sai da ya tabbatar Ummi ta iso asibitin kusan karfe goma snn ya fita, gida ya nufa direct, khadija ce da Samha kadai gidan da yake ranan alhamis ne Khadijar bata je islamiyya ba, Gaishesa khadija tayi ya amsa yace "Samha fah?" Tace "Tana daki" daga haka ta wuce dakin sai ga su sun fito tare, kallonta yake har suka karaso, ya kirkiri murmushi yana kallon khadija yace "We will be back soon khadija, Cafe xamu" daga haka ya juya Samha da ta bi sa da ido ta ji yace "Ki dauko Hijab" juyawa tayi ta koma ta sako hijab dinta ta fito ta samesa yana jiranta waje, idonsa na kanta har ta karaso kusa da shi, yace "Mu je..." Tace "Ummi ta sani" yace "Yeah" daga haka ya kama hannunta suka fice. Mamaki ne ya cika ta ganin inda suka nufo, ya sauka ya ba mai adaidaita kudi, fitowa tayi ita ma tace "Doctor..." Hannunta ya rike ya nufi cikin park din, direct inda ake kiran passenger din Kaduna ya nufa, lkci daya hawaye ya cika idonta cikin sanyin murya tace "Doctor Ummi fa bata sani ba" bai ko kalleta ba bare ya kulata, bbu bata lkci ya biya masu kudin mota, ya nemi bench yyi xamansa kafin motar ta gama cika, can ya kalleta yace "Yea we will be back some other day..." Hawaye sosai take, bata xauna ba har mota ya cika ya mike ya shiga motar, sai da wata mata tayi mata maganar baxa ta shiga mota bane, snn ta shiga ta xauna kusa da matar. Throughout Journey din Abuturrab hirarsa da mutumin da ke kusa da shi yake don mutumin ba dai surutu ba, Samha kam duk jikinta a sanyaye yake, to ina kuma xa su, ganin bata da amsan ba kanta ta hakura kawai, lkci daya bacci ya dauketa. Kusan la'asar suka shigo kd, tana fita mota ta je ta tsaya wani gefe ta rungume hannayenta, shi kuma ya tsaya sallama da sabon abokin da yayi, har suka yi exchanging number da xumar xa su hadu wani lkci idan Allah ya yrda, Mutumin da yace sunansa Bashir yayi ma samha sallama don Abuturrab ce masa yyi matarsa ce, Abuturrab ya karasa yana kallonta yace "Kin gaji koh baby?" Dauke kai tayi bata ce komai ba, yace "Don't worry Sweet baxa mu taba mance Ummi ba, wataran xa mu kai mata xiyara amma as husband and wife, may be with our kid ma then.... Yanxu ina muka nufa?" Sai a snn ta kallesa kmr xata yi kuka tace "Da baka san inda xa mu ba muka taho nan?" Yace "Noo mana baby, yanxu dai mu fara xuwa gun aunt da kika ce tana nan garin koh..." Kallonsa tayi da sauri tace "Da gaske?" Yace "Yea mana, a wani anguwa take?" Tace "Familyn mijinta na can mararraba, lkcn can Abbana ke kai ni, amma wani lkcn suna xama Makera" yace "But mun wuce mararraba ai" shiru tayi bata ce komai ba, can yace "Toh mu je makeran ne ynxu?" Kai ta gyada masa, ya tsayar masu da Napep suka wuce Makera, amma cikin rashin sa'a yan gidan suka ce ai sun ma saki gidan sun koma can maraba, bbu yanda suka iya haka suka fito, Abuturrab na kallonta yace "ki xauna dakalin can dear, xan yi sllh in sama maki abinda xa ki ci sai mu tafi can maraban" xama tayi ta jira yyi sllh masallacin dake layin, ya fito ya nemi shago ya siya mata soft drink da snacks shi ya siya Malt, kallon mutumin dake xaune bakin shagon yana ta xukar taba yake, tunani ya shiga yi me ma yasa ya daina shan abun nn, sai yaji kmr ana tempting dinsa ya siya ya juya kawai ya bar wajen da sauri, taxi ya samu drop da xai kai su har maraban, ba su suka isa ba sai kusan biyar da wani abu, tana gaba yana biye da ita a baya yana kare ma garin da baxa a kira da kauye gaba daya ba kallo, Ita ce ta fara shiga d'an gate din gidan da Sallama ganin ya ki shigowa ta juyo tana kallonsa tace "Come in mana" Murmushi yyi ya bi bayanta, tsakar gida ne madaidaici me dauke da dakuna hudu a jere sai bandaki da kewaye a gefe daya, bbu kowa tsakar gidan sai murhu me dauke da tukunyar shinkafa a kai, kallonsa tayi ya wara mata ido a hankali yace "Shiga mana baby" kallon bangaren bayi tayi jin kmr akwai mutum a ciki sai kuma ta karasa bakin kofar daya daga dakunan dake a matsayin parlor ta bude labulen xaune taga Anty Maryam tana yankan alaiyahu sai wata mata dake kwance tana bacci ta juya baya, sake wukan hannunta tayi ta bude baki tana kallonta, can ta kalli matar dake kwance da Samha ma ke kallo ganin kamar Anty Sarah, mikewa Anty maryam tayi da hanxari ta karasa bakin kofar kawai ta kama hannunta suka fito, turus tayi ganin Abuturrab, ae yana ganin reaction dinta ya gane ba lafiya, murya kasa kasa tace "Ku taho...." Bude wani kofa tayi, dai dai lkcn da Samha taji muryar Mahaifiyarta daga cikin bandaki tana kwalo ma Anty Maryam kira wai ta miko mata zani, ai samha bata jira ta gama bude kofar ba ta shige a mugun tsorace, shi kansa Abuturrab ya rikice ba kadan ba, xae fito da ita daga dakin tun kan ta karasa shiga Anty Maryam da ita kanta a gigice take murya can kasa tace "Ku shiga i will close the door now" hakan yasa Abuturrab ya shiga dakin Anty Maryam ta garkame da makulli ta juya da sauri ta koma parlor tana amsa kiranta. Kuka Samha ta dinga yi tana cewa Abuturrab kashe ta mumy xata yi, bbu irin lallashin da bai yi ba amma kamar yana da da tunxurata duk tayi mugun tsorata gani take kmr Mumy xata fado dakin, shi kansa Abuturrab kansa ya daure ae da kawai Anty Maryam ta bari su fita kawai. Kin koma parlor Anty Maryam tayi don gani take kmr Rachael mahaifiyar Samantha xata ce xata shiga dakin da ta rufe, ai ko tana fitowa tace "Ki duba min kaya a jaka ki kawo min dakin can..." Daga haka ta nufi dakin da su Samha suke, Anty Maryam da gabanta yayi mugun faduwa tace "Anty dakin a kulle yake ai, baban su Asiya ne... Ina jin ajiya yyi" Rachael ta juyo tana kallonta sai kuma tace "Ina ce a bude naga dakin daxu kuma ai Aminu bai dawo gidan nn ba" Tabe baki tayi tace "Toh muje nan din, nagansa very untidy ne" Xaune tayi parlon tana shafa mai tace "Ai Maryam tunda pastor din nan na celestial church jiya yace min ina xaune xan ga Rebecca da musulmin nan very soon hankalina ya kwanta, idan kin kula jiya baccin da nayi har da minshari, rabona da bacci haka fa tun daren da Rebecca ta gudu..." Ta girgixa kai tana wani murmushi tace "Yesu ka ga irin tarbiyar da nayi ma yarinyar nn, yesu nasan baxa ka kamani da laifi ba, Toh kayi gaggawan bayyana min ita!" Ita dai Anty Maryam cukuikuye Alaiyahu kawai take duk hankalinta bai gun, Rachael tace "Ya kina ma alaiyahun haka, tunanin me kike" Da sauri Anty Maryam ta xubar a cikin farantin gabanta tace "Babu komai Anty...." Rachael ta gama xura rigarta ta dau Bible ta fita, Anty Maryam ta bi ta da ido xuciyarta na bugawa. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 48..... Xama tayi tsakar gidan ta bude Bible din hannunta tana dubawa, Anty Maryam ta mike da kyar ta fita tsakar gidan, ta ja kujerar tsugunno ta xauna tana ci gaba da aikin da take, can ta sace kallon Mumy tace "Hayakin nn bai damun ki Anty?" Rachael ta kalleta snn ta kalli Murhun tace "Yo ba gwara ya dame ni ba da xafi ya kasheni a d'an akurkin parlon nn naki Mary.... Ai dai kinga ribar musulunci da auren Musulmi" Anty Maryam ta hade rai tace "Don't start that again aunt, shi da ma Christianityn forcing mutane ake yi su yi?" Tsaki Rachael tayi tace "Mu dama bama bukatar irin ku, ku kare rayuwar ku a musulunci don yesu bai so ku da rahama ba" Tsaki Anty Maryam tayi ta mike ta bar gun ta koma can gaban murhu, Rachael ta tabe baki tace "What a pity" Tunani Maryam ta dinga yi abinda xata ma Mumy taji haushi ta bar gidan ko ma ta wuce church kawai, can dai tace "Ga ku abun tausayi amma ku wani ce kuna tausayin mutum, Astagfirullah... shi Annabi Isan da ku ke bautawa ku ke kiransa da d'an Allah ance maki......" Tsam Mumy ta mike a fusace tana huci tace "Kee Maryam kar ki kai aya, maxa ki tofe yawun bakin ki kan fushin Jehovah ya sakko ya same ki ynzun nn, shi d'an nasa kike xancensa cike da izgilanci??" Maryam ta tabe baki tace "Ni na isa in ma Annabin Allah, ma'aikin Allah izgilanci, ni dai nasan Allahu bai haifa ba ba'a haifesa ba, Annabi Isa kuma messenger dinsa ne haka zalika Annabi Muhammad...." A mugun fusace Mumy ta katse tana hakki tace "Toh kuwa Allah ya tsine maki da wnn furucin, a kan ke musulma ce xa ki dinga fadin wa ennan maganganu, waye kuma Muhammad?" Mikewa Maryam tayi "Annabin Allah ne shi ma, kuma comforter din da Annabi Isa A.S ya gaya maku xai xo, if am nt mistaken bible ne a hannunki, idan kuma baki mance ba nima fa kusan nasan komai a Christianity din nn naku, Anty ki bude john 16:5-8....." Ganin Mumy ba budewa zata yi ba sai kumfar baki take ita a dole an tabo Yesu ta karasa ta karbe bible din ta bude, sai da ta duba tas snn ta rufe bible din tace "Let me make it short, the verse goes thus 'For if i go not away, the comforter will not come unto you, but if i depart, i will send him unto you, and when he comes, he will reprove d world of sin, and approve righteousness nd Judgement..." Murmushi tayi tana kallon Mumy tace "And who is Isa A.S referring to you all as a comforter?? That's prophet Muhammad S.A.W, he is the comforter" Mumy tace "Jehovah ya dawwamar dake cikin duhu, kada ya taba baki ikon gane gaskiya, sha sha sha kawai, talauci kadai ma da ya bar ku da shi ai ya ishe ku" Mai Abuturrab xai yi bnda dariya, sosai Mumy ta basa dariya, ya rike kai ya dinga yi, Samha ta rikesa a tsorace tace "Noo Doctor xa ta ji plss ka dainaaa" hadiye dariyar yayi ya rike baki, Maryam ta tabe baki tace "Ae ba don Allah bai sonmu bane ya bar mu a haka, sai ki ga mu samu in the world here after" Mumy tace "Inaaa ai kwalelanku ku da arziki, baku yrda da d'an sa ba ku ke zaton xai maku arxiki... Baki ganin ynda ubanku ya mutu ko tinkiya daya ba shi da..." Sai kuma ta fashe da kuka tace "Da yau xan ga Rebecca gwara in kasheta in yi layyarta" Anty Maryam tace "Sai kuma ki ga kafin ta dawo ta musulunta, kila har ma ya aureta da ciki jikinta" wani kara da ya firgita sarah dake bacci ta fito da gudu Mumy tayi, Ta isa gun Maryam da gudu ta shakota tace "Jehovah ya isa tsakanina dake, Jehovah ya kona bakin ki da ya furta haka, Jehovah ya hanaki farin ciki da shegen talakan musulmin mijin ki...." Sai kuma ta fashe da kuka tace "Sarah dauko min jakar kayana in wuce hotel, Idan na ci gaba da xaman gidan nn nasan xan shiga fushin ubangijina...." Sarah tace "Haba sis Rachael me ya hadaku haka duk makwabta na ji?" Tura Maryam Mumy tayi ta shige daki sai ga ta ta fito da jakarta tace "Idan kin ga dama ki fito da taki jakar in kuma so kike mu kone a gobarar da xa a aiko masu yau ne sai kiyi ta xama" Daga haka ta fice fuuuu daga gidan, Sarah tace "Maryam me ya faru haka ne" Maryam ta koma kujera ta xauna hade da sauke ajiyar xuciya tace "Toh ma ina na sani magana kawai muke sai naga kuma kmr warce aka ma allura" Sarah ta sa takalmi ta bi bayanta da sauri, murmushi Maryam tayi tayi hamdala a xuciyarta, ba a dau lkci ba Sarah ta dawo ta dau dankwalinta ta daura da jakar hannunta tace "Gobe xan xo Maryam, ban san me ke damun Sis Rachael ba" daga haka ta fice daga gidan, Maryam ta mike ta sa sakata a gidan ta dawo. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By Khaleesat Haiydar📚✍🏻 49..... Da sauri Anty Maryam ta karasa dakin da suke, tana bude kofar Samha ta mike da sauri ta karasa da gudu ta rungume ta, Anty Maryam kam kallon Abuturrab kawai take, Wanda hakan yasa ya mike ya gaisheta, bata iya ta amsa ba don duk jikinta yayi sanyi ganin kyansa da kwarjini amma ya gwammace yayi ta garari sbda wacce addininsu ya sha bam bam, can dai tayi karfin halin cewa "Bawan Allah don me xaka gudu da yar mutane, and what are you up to?" Sauke kansa kasa yyi kamar baxai ce komai ba sai kuma a hankali yace "Saboda ina sonta Anty, so kuma na aure snn ina son musuluntar da ita ta dawo hanya madaidaiciya" Kallonsa kawai Anty Maryam take, ya karasa gabanta yace "Ki yarda da ni Anty ina sonta sbda Allah ba don in cuce ta ba...." Anty Maryam ta girgixa kai tace "Amma kana ganin hakan shine dai dai, rayuwa fa kake da warce ba muharramar ka ba, wanda addinin mu bai yarje mana da haka ba, ka sani amma ka bi son xuciya...." Yace "Noo Anty, i tried my best na ganin ban saba ma addinina ba all through our stay together" tace "Toh me ya hanaka auren nata har ynxu yau wataninku kusan biyu da barin gida?" Kallon Samha yayi sai dai bai ce komai ba, Anty Maryam tace "Kayi shiru?" Yace "Bana son watarana tayi tunanin ina using advantage din aurenta Anty...." Juyawa Anty Maryam tayi ta bar bakin kofar, Samha ta kallesa snn ta bi bayanta, Ko minti biyar basu yi da fita ba Anty Maryam ta dawo dakin, karasawa tayi inda yake ta zauna kan darduman dakin tace "Aliyu koh?" Kai ya gyada mata, tace "Kaga mahaifiyar Samantha na gidan nn ynxu haka nasan tana within,l.. ban san ka ba, ban san daga inda kake ba, ban san halin ka ba, amma nasan kai musulmi ne d'an uwana, hakan yasa xan baka yarda ta dari bisa dari, nasan da baka son Samantha tsakani da Allah baxa ka gwammace irin wnn rayuwar ba, don haka Aliyu kafin ku bar nan ina son ya kasance Samantha matar ka ce ta sunna, if you've tried ur best abiding to the laws of ur religion wataran hakan gagararka xai yi.... In har da gaske kake ka bari a daura maku aure komai xai fi xuwa da sauki" a sanyaye yace "Nima nafi son haka Anty, ban sai san ta inda xan fara bane...." Anty Maryam tace "Dawowar Samantha musulunci ba abu bane mai wahala ni xan taimaka maka, yanxu dai it's better ka tafi ka samu hotel, ita kuma xan kai ta gidan kawata, don mahaifiyarta na iya dawowa nn a ko wanni lkci." Yace "Toh nagode" tace "Amma all this while kuna ina da ita?" Babu bata lkci ya bata labarin d'an rayuwar da suka yi a gombe da Ummi, sai dai bai gaya mata ga abinda yasa suka bar gombe ba sai ce mata yyi kawai ziyara suka xo kawo mata" Ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh shknn Aliyu Allah ya maku jagora, ni nafi kowa farin ciki da abunda ya faru Allah yasa lkcn fitowar yayana daga 6ata ne ya xo, Allah yasa ta dalilin haka ya gane gaskiya" Abuturrab yace "Ameen" mikewa tayi tace "Bari in xubo maka abinci" daga haka ta fita. Shinkafa da wake da mai da yaji sai kayan vegetables a kai ta kawo masa da ruwa a jug, yayi mata godiya ta fita. Mai gidanta ta kira ta sanar da shi komai ta kuma bukaci ya dawo don su hadu da Abuturrab, bayan yan mintuna ya shigo gidan, a tare suka shiga gun Abutturrab, ya gaida mai gidan nata da ladabi, Duk suka xauna dakin, Mijin Anty Maryam mai suna Aminu da ke ta kallon Abuturrab yace "Sannu da xuwa bawan Allah" Abuturrab yayi murmushi yace "Nagode" tambayoyi kmr yanda Anty Maryam tayi masa ya shiga yi masa shi ma, sosai mijin Anty Maryam ya jinjina karfin hali irin na Abuturrab daga karshe shi ma ya nuna gwara kawai ayi auren komai xai fi xuwa da sauki. A can Gombe kuwa tunda Ummi ta dawo Khadija ta fadi mata ai fa tun safe Abuturrab suka fita da Samha, jikinta yyi sanyi don lkci daya ta fahimci tafiya yyi da ita barin da taji wayarsa kashe tun daxu, amma bata nuna ba ta shige bedroom kawai ta kwanta tana tunanin wani rayuwar kuma xa su yi. Sun yanke akan cewa gobe Abuturrab xa su je gun mai gari da Mijin Anty Maryam daga haka kuma Anty Maryam tace ya wuce hotel kafin Mahaifiyar Samha ta dawo ita kuma xata je kai Samha gun kawarta, Sallama yayi masu ya fita, sai dai bai ji ddin rashin ganinta ba har ya bar gidan ita ko tana parlon aunt din tata bacci ya dauketa. Karfe shidda Anty Maryam ta sa ta shirya bayan tayi wanka ta bata nikab da hijabi snn suka fita a lkcn ma yaranta sun dawo daga islamiyya, bata bari sun lura da Samha ba har suka bar gidan, Addu'a Anty Maryam ta dinga yi Allah yasa Rebecca bata anguwannin don tana da kawaye yan coci kamar ta sosai a wajajen, tana rike da hannun Samha sai sauri take su isa bakin titi ta samu machine su hau, ta layin da ke gefensu taji an kwada mata kira, ta juya da sauri cike da faduwar gaba ta ga Sarah ce tsaye kofar wani gida, Anty Maryam da ke ci gaba da jan hannun Samha da ta tsorata ita ma taki tsayawa tace "nan kika xo ashe" ganin Sarah na tahowa yasa hanjin cikinta yayi mugun kadawa tace "Gani xan xo yanxu, bakuwa xan raka" Sarah da har ta kusa isowa gun su sbda saurin da take tace "Sis Rebecca nake jira tun daxu wllh, haba tun fa daxu fada take...." Tuni Samha ta janye hannunta a na Anty Maryam tayi gaba ko ina na jikinta na rawa, Sarah ta bi ta da ido, Anty Maryam na ganin haka ta tsaya gabanta ta ynda baxa ta dinga ganin Samha ba tace "Toh ko mu je in bata hakuri ni fa ban san me ya faru ba" Sarah tace "Jesus, yarinyar nan yanayin Samantha gareta, wacece ita?" Anty Maryam tayi dariyar yake cike da karfin hali tace "Samantha da Nikab kuma? yar wata uwar daki na ce... Haka take fama da rufe fuska" Sarah dake ta kkrin sake kallon Samha da tayi nisa sosai tace "Har tafiyar fa Maryam, Jesus of Nazareth" Maryam tace "Ohh don dai Samanthar ce a ranki, ynxu mu shiga in ba sister hakuri sai ta iya hada ni da yaya" Daga haka ta ja hannunta suka nufi gidan, Suna shiga Maryam tayi wani salati tace "Amma yarinyar nn Sha sha sha ce kinga kudin motar fa a hannuna bata karba ba" Sarah tace "Ayya to kiyi sauri ki isketa mana" bata rufe baki ba Maryam ta fice da sauri tace "Ina dawowa ynxu" Can bakin titi ta iske Samha ta rakube jikin wani shago, bbu wata wata ta tsayar masu da machine biyu ta fadi inda xa su suka hau suka bar gun tana hamdala a xuciyarta. *Haske writers asso* Plss ana min uxuri na rasa ynda xan dinga squeezing time ne, snn kuma there is shortage of power a inda nake ynxu wllh shi yasa yake taking time. 💫 *Noorul Huda*💫 By Khaleesat Haiydar📚✍🏻 50...... Suna isa gidan Anty Maryam ta shiga Samha na biye da ita a baya, Anty Maryam suka gaisa da aminiyar tata mai suna Amina daga haka tace mata xata bar Samha nan gidan xuwa gobe ta xo ta dauketa, bbu bata lkci ta bar gidan ta koma gida. Wani hotel Abuturrab ya samu yyi lodge, da ya tuna abinda ya faru gidan Anty Maryam sai abun ya basa dariya, sai dai hankalinsa ya kasa kwanciya ya rasa dalili, yana yin magrib Coffee kadai ya iya sha ya dawo room dinsa. Karfe takwas da yan mintuna Ummi na xaune daki gaban computer sai dai gaba daya hankalinta bai kai, sosai su Abuturrab suka tsaya mata don bata san halin da xa su je su shiga ba kuma, jawo wayarta tayi for the 5th time within that period ta sake dialing numbersa amma switch off ta dafe kai, bude kofar dakinta aka yi ta dago da sauri Yusuf ya karaso ya xauna kujera yana kallonta yace "Sannu da aiki Ummi" ba tare da ta kallesa ba idonsa a kan screen din computer tace "Yauwa" Ya d'an yi murmushi yace "Ummi kar fa ki sa ma kanki damuwa, dama ni ina ganin Aliyu nasan ba shi da gaskiya, as in the way he does his things ma xaka gane hakan, baka taba gane abinda ke ransa na lura, he can be a silent killer, at the first place na tambayeki hadinsa da Samha kika ki gaya min, daga bincikena tun a jiya na gano Samha ba matarsa bace, though bance xaman banxa suke ba, amma daga duk alamu rabo ta da iyayenta yayi may be for his selfish interest, tun daga lkcn da kika ce min bai ji na fara gano wasu abubuwan.... But Ummi me yasa kika boye min kilan da hakan da ya faru ynxu bai faru ba, i would have kept an eye...." Kallonsa Ummi tayi a karo na farko tace "Bana son xancen Yusuf" mikewa yayi yace "Aiit, buh am gonna fish him out idan Allah ya yarda" daga haka ya fita. Anty Maryam na xaune tsakar gida a ranan tana wanke kwanukan da suka ci abinci amma hankalinta na ga tunanin decision din da suka yanke da mai gidanta na aura ma Aliyu Yar d'an uwanta, bude kofar soro aka yi ta juya da sauri taga Rachael ce da Sarah, Duk da ba wuta tsakar gidan sai hasken wata hakan bai hanata ganin yanda Rachael ta daure fuska ba tana tahowa kamar xata tashi sama, Anty Maryam ta dauke kai tana murmushi ta ci gaba da wanke wankenta, sarah ce kadai tayi mata sannu da gida suka shige parlor, Anty Maryam ta mike ta dau abinci ta kai masu ta fito, ko da ta gama wanke wanken xamanta tayi tsakar gida tana sake saken yanda al'amarin gobe xai kasance, can ta mike ta shiga dakin mai gidanta ta xauna tana kallonsa tace "Abbansu Asiya ya kake ganin xa ayi gobe ne wai" Yace "Gun mai gari xa mu je a daura auren sai su tafi duk inda xa su, matukar xai iya kula da ita, na kuma ga yana sonta sosai don da ganinsa kasan ba karamin mutum bane." Da damuwa tace "To fa bata amshi musulunci ba har ynxu" yayi murmushi yace "Ba yar ki bace kin san yanda xa ki bi da ita ai, sai dai kuma kada a tilastata don in har aka yi haka tana iya komawa gidan jiya tun da ba da son ranta ba.... Ko kin mance yanda muka yi da ke Maryam" ganin dariyar da yyi ta hade rai tace "A'a ni baka aureni a Christian ba ni musulma ce a lkcn ma" yace "Amma a lkcn abubuwan da kike yi meye banbancin ki da Christians din, ba fa gori nake maki ba rabin rai kawae dai magana ce" ta tabe baki tace "Ae don ina gun yayana ne lkcn Kuma mahaifiyar Samantha ce matsayin uwata...." Yace "Toh kar ki ji komai ni nasan da kanta xata yi sha'awar addininmu ba sai an mata dole ba, at the first ma da bata son musulunci baxata yarda da musulmi ba har su gudu tare ta bar iyayenta" Anty Maryam tace "Haka ne, kuma kaga lkcn da take xuwa hutu nan bata kin yi duk abinda na sa ta tun daga kan sllh har xuwa tafiya islamiyya da su Asiya" yace "Toh kin ga" Mikewa tayi tace "Bari in je can parlor" daga haka ta fita. Washegari da ya kasance friday da safe Abuturrab ya fito ya nemi d'an boutique ya siya kaya da kudin dake hannunsa, daga haka ya nufi Atm machine don cire kudi, takaici ne ya ishesa don Atm machine din da ya gani bai fi biyu ba kuma duk ba kudi, kallon agogon hannunsa yayi yaga tara bata yi ba, kawai yayi deciding ya wuce cikin kaduna kawae, sai da ya koma hotel ya shirya snn ya dau hanya, yana isa ya kunna wayarsa tunawa da yyi sun yi exchanging number da mijin Anty Maryam, yana cire kudin ya shiga tunanin me xai siya kuma kafin ya koma wayarsa ya shiga ring Sadeeq ya gani jikin Screen din, har ya fara tunanin waye kuma sadeeq kawai ya tuna gayen da suka hau mota tare tun daga gombe, dagawa yyi, nan suka gaisa da fara'a Abuturrab yace "Kasan jiya fa can maraba muka wuce amma yanxu ina cikin kaduna na xo cire kudi..." Sadeeq yace "Au haba, a ina kake yanxun?" Abuturrab ya kalli gun yace "Ina bypass" Sadeeq yace "Haba to ka karaso nan gidanmu mana kafin ka koma" Abuturrab ya kalli agogo sai dai bai son Sadeeq ya ga kamar yyi shun dinsa, yace "Funny you, ni da nake sauri" Sadeeq yace "Sai in kai ka har maraban da motata" Abuturrab yyi jim don bai son exposing secret dinsa ma kowa kuma, can dai yace "Haba don xan xo gidan ku sai ince sai ka mayar dani, bari in taho sharp sharp in koma ba sai ka yi wahalan kai ni ba" Sadeeq yace "Alryt" address ya tura ma Abuturrab da yake yasan garin xuwa gidan bai yi masa wahala ba sai dai ba dai nisa ba don sai kallon agogo yake, babban anguwa ce ta masu abun hannu, Sadeeq ya fito daga wani kantamemen gida mai dauke da gate biyu kai da ganin gidan kasan naira ya xauna, nan suka gaisa sadeeq na dariya yace "Ashe dai xaka gane..." Abuturrab yace "Haba dai ai ba wani wahala" daga haka suka shiga gidan sadeeq ya kai sa har babban parlon gidan, Abuturrab na xama ya ji gabansa na faduwa ya rasa dalili, Sadeeq na kallon kanwarsa da ta fito yace "Kiyi setting mana breakfast a bedroom dina" tace "Toh" sannan ta gaida Abuturrab ta koma kitchen, Sadeeq yace "This is our home, you feel free frnd" Abuturrab yayi murmushin karfin hali yace "Sure" Ana bude kofar parlor ya waiga da sauri kamar jira yake, bai san lkcn da ya mike tsaye yana kallon mutumin dake kallonsa shi ma a bakin kofar ba, Sadeeq ma ya mike yace "He is my Dad...." Abuturrab ya kallesa ya kirkiri murmushi yace "Ohh alryt" juyawa Mutumin yyi ya fita, nan hankalin Abuturrab yayi mugun tashi, ya dake ya koma ya xauna, Sadeeq dake ta studying dinsa yace "Any problem Aliyu?" Wara ido yayi yace "Ohh nothing Sadeeq" ba a dau lkci ba mutumin ya dawo parlor, sai a snn Abuturrab ya gaida shi kansa a kasa, mutumin ya amsa yayi wucewarsa Sama, mikewa Abuturrab yyi yana kallon Sadeeq yace "Let me answer a call in dawo" daga haka yayi waje da sauri, wani mugun faduwa gabansa yyi ganin mutanen da bai gani ba lkcn da xa su shigo tsaye bakin gate wato dai soldiers in uniform, dakewa yayi ya karasa xuciyarsa na bugawa ganin kallon da soldiers din ke masa kawai ya juya ya koma ciki da sauri yana furta innalillahi a xuciyarsa, Yana shiga parlorn ya isa gun Sadeeq da sauri, Sadeeq ya mike da sauri ganin tashin hankali bayyane fuskarsa yace "Aliyu lafiya" Abuturrab yace "Nooo, help me out now plss!! ur dad.... Abokin Abba na ne" Sadeeq dake kallonsa da mamaki yace "Then?" Abuturrab ya kamo hannunsa yace "Don Allah make a way out for me nayi ma Abbana babban laifi i left home for months, nasan kilan yanxu ya ma kirasa wllh.... Plss" tsit Abuturrab yayi ganin Col Ishaq yana saukowa stairs, da sauri sadeeq yace "Haba to meye baxa ka hau sama mu yi break ba sai a nan frnd, plss mu tafi bedroom dina, it will be more convenient there." *Haske writers asso* Afuwan for the delay 😎 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 51..... Abuturrab ya gyada kai yana kirkiran murmushi yace "Toh... toh mu tafi dakin" Ta gefen mahaifin Sadeeq suka wuce xuwa dakin Sadeeq din, Sadeeq ya sa ma kofar key yace "Shitt, ohh God, i caused everything" Abuturrab kam xaunawa yayi kan gado ya rike kai, Sadeeq ya nufi Balcony din dakin da sauri yana kallon kasa ya girgixa kai ganin prickled Object dake watse a kasa wanda sbda shi aka xuba su, dawowa daki yyi yana tunanin hanyar da xa su bi su bar gidan don yasan duk Abbansa ya sa an toshe hanyoyin da yake bi, can ya dafe Abuturrab yace "Chill guy sai dai idan ba sojoji suka haife mu ba, we will surely find a way out, look... bana daukar last a irin haka fa, ni nan da kake gani ko kama kafata baka yi ba gun rashin ji, don haka in sha Allah sai mun fita" Abuturrab ya kallesa sai yyi murmushi yace "Yea kuma haka ne, buh we have to be very fast frnd" Sadeeq ya isa kusa da kofarsa ya bude a hankali tsaye ya ga Dad dinsa corridor din, pretending yyi yace "Abba you are here dama" Dad dinsa bai tanka sa ba, sadeeq ya shiga bedroom din mum dinsa, Kanwarsa Sumayya ce ke dakin tana gyara, yace "Sumy Umma fah?" Sumayya tace "Tana kitchen," shiru yyi sai kuma ya bude balcony din Ummantasa yana leken kasa, can ya dawo ya fara bude drawers dinta yana bincike, Sumy ta ja ta tsaya tana kallonsa da mamaki, ya kusa minti biyar kafin ya dago ganin kallon da take masa ya jawota a hankali yace "Pls Sumy am in trouble ki taimake ni" da mamaki tace "Me kuma kayi" murya can kasa yace "Ni da frnd dina wllh. Ga Abba can yana gadi a corridor kar mu fita" tabe baki tayi tace "You again" da damuwa yace "Plss" tace "Toh me xan maka" a hankali yace "Fita xa kiyi idan kin kai parlor sai kiyi ihu sosai kamar kin fadi din nan nasan Abba xai sauka daga nan ni da shi sai mu shigo nan mu dira ta balcony that's all, idan mun fita sai mu san next action" Sumy da ta saki baki tana kallonsa tace "Tabdi, to me ku ka yi" yace "Plss mana angel" tace "Noo ni ba ruwana baxan yi ba" wayarsa ya fiddo lkci daya yayi mata transfer din dubu hamsin, Ya dau wayarta dake kan mirror ya mika mata, karba tayi ganin alert ta bude ido tace "Har da bribing" ya langwabar da kai yace "Haba sisterna dama muna haka da ke" shiru tayi sai kuma tace "Toh ni dai bbu ruwana, idan kuma aka gano karya nayi fa!" Sadeeq yace "Haba kin fa iya pretending baby, kin ga muna bata lkci plss" turo baki tayi tace "Toh" yace "Yauwa sis of life" daga haka ya fita, waya ya tarar da Abba ke yi ya shige dakinsa kawai, mikewa Abuturrab yyi yana kallonsa, yyi murmushi yyi patting shoulder dinsa yace "Chill na samo mana hanya" gaban madubi sadeeq ya nufa ya bude ya fiddo lighter daga haka ya koma ya xauna yana jiran jin ihun kanwarsa, Can dai ya kalli Abuturrab yace "Hope ka iya dirowa daga sama xuwa kasa" Dariya Abuturrab yyi yace "Sure" Dai dai nn suka ji wani uban ihun da Sumy tayi wanda sai da gidan ya amsa, sai da sadeeq ya jira har second goma snn ya bude kofa ya ga ba Abbansa ya yafito Abuturrab suka shige dakin Ummansa da sauri ya bude Balcony, Abuturrab ne ya fara Dira kasa snn shi, Ya nufi gun da ake ajiye generator din gidan da sauri ya kinkimo gallon din mai dake ajiye gun ya isa gun flowers, da mamaki Abuturrab yace "Hey! What re you trying to do" Sadeeq bai kulasa ba ya xuba fuel kadan jikin flowers din ya mayar da gallon din snn ya dawo ya yanko wani flower mara fuel ya kunna masa lighter, sai da ya kama snn ya jefa kan flowers din da ya xuba ma fuel, lkci daya wuta ya kama, kama hannun Abuturrab yyi da sauri suka xaga xuwa daya side din suka shiga bayan wasu flowers ta yanda xai iya dinga hango gate, kan kace me daya barin ya fara ci da wuta sosai wanda hakan ya ja hankalin soldiers dake bakin gate suka taho da sauri suna raising alarm, Sadeeq na ganin gate wayam ya kalli Abuturrab yace "Gudu sosai fa xa mu yi" daga haka ya mike haka ma Abuturrab, a dari da sittin suka isa gate a kan idon Abban Sadeeq da ya fito da sauri jin alarm din soldiers dinsa, sake baki yyi yana kallonsu har suka fice, kamar masu gudun relay race suka isa bakin titi suka afka Adai daita sahu, sai a snn Sadeeq ya dinga kyal kyala dariya, Abuturrab kam lumshe ido kawai yyi yana murmushi. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 52..... Bude ido Abuturrab yyi har lkcn yana murmushi ya kalli Sadeeq yace "Kai babba ne!" Yar dariya Sadeeq yayi yace "That's the only way out ae" Abuturrab yace "Uhm amma komawar ka gida bbu rana koh?" Sadeeq yace "Haba daii ko anjima sai naje, amma da Thummun bukumun xan shiga...." Dariya Abuturrab yayi yace "Really!" Sadeeq yace "But wani laifi ne kayi haka har ka bar gida for 2months, ni fa duk abinda xanyi ban wuce 2days a waje xan samo solution in yi komawa ta gida kuma lafiya lau" Abuturrab yyi murmushi bai ce komai ba, Sadeeq yace "I might find a solution for you kar ka ji komai ka gaya min" Abuturrab yace "You know Col Ahmad ur dad's frnd?" Sadeeq ya d'an yi shiru can yace "Na kano?" Abuturrab yace "Yea kasan shi?" Sadeeq yace "Wait! Don't tell me u re his son, don't tell me kai ne wanda ka gudu da yar mutane for months?" Kallonsa kawai Abuturrab yake, Sadeeq ya kalli me Napep da sauri yace "malam malam tsaya nn" Mai adai daita ya ja ya tsaya, Sadeeq ya fita yana kallon Abuturrab dake kallonsa shi ma, can ya fashe da wani dariya yace "Kaiii.... ashe da babba nake tare da...." Dariya Abuturrab yayi ya fito daga adai daitan Sadeeq yace "Waow... kasan da naji abinda kayi na dde ina son in gan ka ko a hotone, gaskiya kai babba ne, nasan duk yaran abokan Abba na amma banda kai how comes, kai ne wanda i think 2 years back ku ka yi fada da yaron wani minister a Uk" Abuturrab ya ba mai adai daita kudinsa ya kalli Sadeeq yace "Ai ni ban taba attempting kona gidanmu ba, kaga kuwa kai ne babba" Dariya Sadeeq yayi yace "Toh wai ina yarinyar yanxu.... Kaiii don't tell me ita ce na gan ku tare jiya?" Abuturrab yace "Yea..." Sadeeq ya xaro ido yace "Bari muyi lodging hotel kayi gist dina plsss in kara course and probably in samo maka solution" Abuturrab yace "Maraba xan wuce yanxu haka it's very urgent" Sadeeq yace "Haba, bari in kira frnd dina ya kawo mana mota sai mu je i really want us to be frnds" Murmushi Abuturrab yyi kawai, cikin minti Sha biyar aka kawo masu mota suka dau hanyar maraba, Sadeeq ke driving din, Abuturrab ya kallesa yace "But pls let this be a secret between us plss, i don't trust easily sai gashi nayi trusting dinka lokaci daya don't betray that" Sadeeq yace "C'mon baka da damuwa frnd," Abuturrab yace "Amma idan ka koma gida Abba ya tambayeka inda nake me xaka ce?" Sadeeq yace "I don't know ur whereabout and that's it" Abuturrab bai kuma cewa komai ba lkci daya Samha ta fado masa, yasan period dinta yau ne ko gobe don ya ga changes jikinta, tunanin hakan yasa hankalinsa yyi gunta gaba daya. A can maraba kuwa tunda Samha ta tashi ta kasa fitowa sbda ciwon ciki, duk a tunanin Anty Amina bacci take, tun tana daurewa har ta kasa ta fara juye juye wajajen karfe goma, yarinyar Anty Amina na ganin haka taje ta kira Uwarta, tsaye tayi tana kallonta tace "Me ya faru yar nan?" Cikin kuka Samha tace "Cikina" tace "Ikon Allah, yana maki haka ne dama?" Kasa bata amsa tayi sai kuka, can ta mike da sauri ta fita jin amai na taho mata nan ta dinga kwarara amai bakin kofar, Anty Amina da abu kadan ke rudata barin yanda taga tana aman ta dau gyale ta fice da sauri, machine ta samu bata dire ko ina ba sai gidan Anty Maryam ta fada gidan da gudu, Anty Maryam na sharan tsakar gidan amma duk hankalinta bai gun, tsoronta daya kada Abuturrab ya xo gidan mahaifiyar Samantha na nan, mijinta har ya gaji da jira ya fita, sis Rachael kam na xaune bible hannunta ana karatu tsakar gidan, Anty Maryam na ganin kawarta ta mike da sauri, Amina na haki tace "Maryam kada yar mutane ta mutu min a gida in shiga uku ki taho mu je yar da kika kai min kar ta mutu" Maryam da ta rikice tace "Me ya faru, me ya sameta?" Amina ta fashe da kuka tace "Ki taho mu je amai take ta yi wai cikinta" Rachael tace "Wace yarinyar kika kai mata?" Anty Maryam da gabanta ya dinga faduwa duk ta rikice ta shiga ciki da sauri don dauko hijab, Amina na kallon Sis Rachael tace "Mama taso mu je kar wani abu ya faru in shiga uku" mikewa Rachael tayi xata bi bayanta Anty Maryam ta fito da sauri tace "A'a sister ba sai kin je ba, kiyi xaman ki gida," Rachael ta watsa mata wani kallo tace "Ai ba ke kika gayyato ni ba, kuma rai xan je ceto...." Daga haka ta bi bayan Amina da har ta fice. Tsaye Sadeeq yyi da motar inda Abuturrab yace ya tsaya, Abuturrab ya bude motar ya fito yana kallon kofar shiga gidan, Sadeeq ma ya fito yana kare ma garin kallo, dai dai lkcn da Anty Amina ta fito Rachael na biye da ita a baya, ido hudu suka yi da Abuturrab, still tayi inda take tana kallonsa ko kiftawa bbu, xuciyar Anty Maryam ya kusa shigewa cikinta ganinsa ita ma, kmr xata tashi sama ta bar gun ta nufi titi, Abuturrab kam kallon sadeeq yyi yace "it's nt safe here....." Daga haka ya bude mota ya shige haka ma sadeeq suka ja motar, wani ihu Rachael ta saki ta bi motar da gudu. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 53...... Ko kafin su isa titi har Anty Maryam ta hau machine, Abuturrab ya bi bayansu, gidan bbu wani nisa, Anty Maryam bata kulasa da shi ba ma ta shige gidan, bbu wata wata tasa ma Samha dake ta juye juye har lkcn Hijab snn ta ja ta suka bar gidan, sosai tayi mamakin ganin Abuturrab, shi dai sadeeq d'an kallo ya xama, Abuturrab ya gaisheta yace "Anty in tafi da ita kawai, let me get her drugs" tana kalle kalle tace "Ina xa ku tafi?" Yace "Ba nisa xa mu yi ba, beside it's nt safe here kinga mum ta gan ni" sake Samha tayi a sanyaye, ya kama hannunta ya bude mata bayan mota ta shiga, Sadeeq ma ya shiga motar daga haka suka bar gun Anty Maryam na kallonsu, daga jiya xuwa yau har ta rame tsabar tension, ko minti uku basu yi da barin wajen ba Machine din Anty Amina da Rachael suka iso gun, xuciyarta ya dinga bugawa har Rachael ta sakko fuskar nn nata shabe shabe da hawaye, ta shako Anty Maryam tace "Maryam yaron da ya dauke Rebecca na gani kofar gidan ki, wato kina da masaniyar inda 'ya ta take kika bari ina ta gantalewa a duniya ko, ashe ke munafuka ce Maryam dama addininku har da munafurci yake koya maku...." Anty Maryam tace "Wani magana kika haka sister, waye kika gani kofar gidana, ce maki yyi wajena ya xo?" Rachael ta fashe da kuka sosai tace "Me nayi maku xaku raba ni da ya ta, idan bae san ki ba me xai xo yi kofar gidan ki" Anty Maryam tace "Yau naga ikon Allah, sister ki yrda ni ko sanin kamaninsa bnyi ba, idan ba dai ko ranan ya fara xuwa ba ko kuma ita tayi masa kwatancen nn.... Ni bn san irinsa ba, taya xan hada kai gun cutar da 'yar d'an uwana Sister, i know nothing about him" Rachael ta dinga rusa kuka tana cewa "Toh kuwa idan ba gizo yyi min ba ni dai na gansa a kofar gida da mota... Kila da gasken ita tayi masa kwatancen nn din" Anty Amina dai tunda suka sauka ta shige gida ta bar su tsaye, sai gata ta fito da mamaki tace "Maryam bn ganta ba kuma?" Anty Maryam tace "Machine na sa ya kai ta gida, dama yarinyar kawata ce ta xo xata kwana can gidana kuma ina da baki shi yasa na kawo maki ita nan" Ko sanin abinda suke cewa Rachael bata yi ba sai rusa kuka take tana tsine ma Abuturrab, Anty Maryam ta kamo hannunta tace "Kiyi hakuri sister in har dai shine ya xo kofar gidana to wataran xae sake dawowa kilan don ya gan ki ne shi yasa ya koma" da kyar ta ja ta suka bar gun don komawa gida, a xuciyarta kuwa gode ma Allah take da Abuturrab ya wuce da ita. Lodge din da ya sauka Abuturrab ya nufa, Sadeeq yace "Haba she's in pain mu tafi asibiti mana guy?" Abuturrab yace "She'll be alryt idan Allah ya yrda....." Suna isa hotel din Abuturrab yasa ta fito suka shiga yana rike da hannunta, Sadeeq na biye da su a baya, kwanciya yasa tayi kan gado, Abuturrab ya kalli Sadeeq yace "Mu je in siyo mata magani frnd" Sadeeq yace "Damn it, kai likita ne da xaka ce xaka siyo mata magani kaga yarinya is in pain why baxa a je asibiti ba?" Abuturrab yace "Yea am a doctor i knw what to get her, you don't wrry" mikewa Sadeeq yyi sai kuma yace "Haka to xa a bar ta ita kadai??" Rasa abun cewa Abuturrab yyi, lkci daya yaji wani iri har cikin ransa, can ya dake yace "Ohk ohk, u stay...." Daga haka ya fice ba don hakan da yace ya kai har xuciyarsa ba. Sadeeq mai shegen tausayi nn ya xauna ya dinga mata sannu, ko kadan bai son ganin mace bata da lfya, ko cikakken minti goma Abuturrab bai yi ba ya dawo, Sadeeq na tambayarsa har ya dawo bai tanka sa ba ya ajiye ledan hannunsa ya durkusa kusa da ita yana kallonta, can ya kalli Sadeeq ya ciro kudi ya mika masa yace "Plss abinci xaka d'an samo mana ta ci kafin in bata magani" mikewa yyi yace "Ohk, am with cash" daga haka ya fita, kafin ya dawo har Abuturrab yasa ta kintsa yayi mata allurorin da xai yi mata, ko da ya shigo bacci take. Sadeeq ya ajiye abincin hannunsa yace "How is she now?" Abuturrab yace "She's fine" Wayar Sadeeq ne yyi ring, ya fiddo ya ga sabon number ke kiransa, kallon Abuturrab yyi, Abuturrab dake kallonsa shi ma yace "Who?" Sadeeq ya daga kafada xai daga Abuturrab ya taso da sauri ya karbi wayar yana kallon screen, wani mugun faduwa gabansa yyi ganin number Abbansa ne, ya koma ya xauna yace "It's my dad's number" Sadeeq ya xaro ido yace "Haba dai, shud i pick?" Jin Abuturrab bai ce komai ba ya daga kiran ya sa hands free, daga daya side din Abban Abuturrab yace "Abbakar?" Sadeeq ya gyara xama yace "Na'am ina kwana?" Bai amsa gaisuwarsa ba yace "Ka gane me magana kuwa?" Sadeeq yace "A'a ban gane ba" Abba yace "Haba?" Sadeeq ya d'an sosa kai yace "Lah kamar muryar Abban kano! Sae yanxu na gane" Abba yace "Ina Aliyu, ba shi nasan kuna tare" Abuturrab ya girgiza masa kai da sauri alamar yace baya nn, Sadeeq yace "Abba tun daxu muka rabu yace min sokoto xai je, Abba wllh ban san shine Aliyu ba, i wouldn't have done what i did, i never knew him coincidentally muka hadu a mota daga Enugu xuwa nn kaduna da shi har muka yi exchanging number, Wai ashe...." Katse sa Abba yayi yace "Good, you tell him that ni nace ka gaya masa har ya bar duniya kada ya sake ya bari mu hadu, either by mistake or not, in har ya bari hakan ya faru sai dai wani ba shi ba" Sadeeq dake ta sosa kai yace "Bai kai ga haka ba Abba kayi....." Abba yace "Kai ma idan ka shigo hannuna sai na lahira ya fi ka jin ddi, makaryacin banxaa" katse wayar sadeeq yyi yana yar dariya, Abuturrab kam murmushi yyi, Sadeeq yace "Ai mun saba jin irin haka tun muna yan kanana ko frnd" Aliyu ya daga kafada yace "Sure!" Mikewa Sadeeq yayi yace "Muje daga waje ka ban lbrin how all this happened... I don't want us to disturb her tunda tana bacci" mikewa Abuturrab yyi suka fita. A haraban hotel din suka xauna, dai dai lkcn da wayar Abuturrab ya fara ring ya kura ma number ido kafin ya daga ya kai kunne, muryar mijin Anty Maryam yaji yana cewa "Aliyu kar ka shigo unguwar mu yau, ka jira har sai na kira ka kafin ka xo" a hankali Abuturrab yace "Toh" nan da nan ya gano da matsala knn. Lbrin yanda suka hadu da Samha ya shiga basa tun daga farko, Sadeeq ya xaro ido yana kallonsa jin ba ma musulma bace, Abuturrab dai ya rasa gane me yasa xuciyarsa ya kasa samun nutsuwa sai faduwa gabansa yake, bada lbrin kawai yake amma hankalinsa bai gun, Sadeeq ya lura da hakan yace "Any problem?" Abuturrab ya shafa kansa yace "Am just tired frnd" ko rufe baki bai yi ba wayarsa ya dau ring, da sauri ya daga hade da sallama ganin number Hajiya Mariya, bata amsa sallamar ba tace "Aliyu me kaje yi kaduna kuma? Kana ina yanxu haka? Where r you now" bai kai ga bata amsa ba yaji an bude gate din hotel din, duk suka kalli direction din da Sadeeq mota ce guda na soldiers, mikewa suka yi da sauri a tare kmr hadin baki suka kalli junansu, lkci daya duk suka nufi cikin hotel din da sauri, Sadeeq yace "Damn it, damn it.... anyi tracing dinmu" Daki suka shige Abuturrab dake ta furta innalillahi a xuciyarsa ya nufi window da sauri yana lekawa ko akwai wani hanya da xa su bi su fita, Ganin bai ga alamar hanya ba ya koma ya xauna gefen gado ya rike kai yana kiran Allah a xuciyarsa, y is all this happening to him, me yasa abubuwa ke wargaje masa haka, me yasa har ynxu aurensa da Samha yaki yiwuwa, Maminsa ce ta fado masa jikinsa yayi sanyi sosai, may be that's the reason, Sadeeq yace "Haba kar ka karaya soon Aliyu, we will get the hell outta here, ba wanda ya isa ya kamani am nt ready for that now.... I will get a way for us" Wayarsa ya ciro da sauri ya bude ya cire sim ya jefa aljihu yace "Damn this..." don yasan duk ynda aka yi ta haka ma aka yi tracing din nasu, kofa ya bude da sauri ya fita Abuturrab ya bi sa da ido, yea hakkin mahaifiya. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 54...... Ta bayan hotel din Sadeeq ya fito ya dinga tafiya yana kalle kalle har ya kusa xagawa, da karfi yace "Shit..." Ganin gate daya gare hotel din, ya kalli fence din da yake tunanin kila akwai wuta jikin wire din kai, neman change over ya dinga yi bai gani ba, ganin kara bata lkci yake kawai ya juya ya koma ciki da sauri, wani kofa daga kofofin dakunan hotel din ya bude yaga wata mata xaune da yaranta biyu suna cin abinci, sai wani da dukkan alama mijinta ne yana danne laptop, duk suka saki baki suna kallonsa, ya karasa da sauri ciki yace "Emm, don Allah taimako sbda Allah, emm tare da step sis dita nake kuma room daya na kama har da frnds dina naga kamar family ne ku, plss ta d'an tsaya nn xuwa anjima xa mu wuce plsss, sorry i intruded just like that, Assalamu alaikum" matar da miji dai sai kallonsa suke sun rasa abun cewa, juyawa yyi da sauri ya koma nasu dakin, Abuturrab na nan har lkcn yanda yake a xaune da alama idea ya gama kare masa ne gaba daya, Sadeeq ya shiga tashin Samha, tana bude ido ta mike xaune da sauri tana kallonsa, yace "Look we re in trouble you just follow me, we need to get out of here now....." kallon Abuturrab dake kallonta tayi, ya gyada mata kai alamar ta bi sa duk da bai san inda xai kai ta ba, daga haka Sadeeq ya ja ta suka fice daga dakin yace "Bathroom xa ki shiga idan mun je dakin kuma kar ki fito, don't try coming out" Yana bude dakin suka shiga ya kirkiran murmushi yana kallon couples din ya hade hannuwansa yace "Toh mun gode kwarai ga ta nn" Daga haka ya nuna mata bathroom, ita ma da ganinta kasan a tsorace take ta shiga bathroom din Sadeeq ya juya ya fice ya koma nasu dakin yace "Let get out of here Aliyu ga su can a reception" daga haka ya kama hannunsa suka fice ta baya, Wani uban tsalle Sadeeq yyi ya tabo wire din fence yaji ko da wuta yaji bbu yace "Yess" Abuturrab dake ta kalle kallen gun ya nufi gun wani ladder karama da alamar na hawa ayi trimming dogayen flowers din hotel din ne, da sauri ya karasa gun handgloves da masu aikin ke sa wa ya saka har uku, snn ya dawo ya hau ya d'an taba wayar yaji bbu shocking, da karfi ya ja wayar yyi baya sosai wanda har sai da yaji yayi piercing din hannuwansa duk da hand gloves din amma bai damu ba ya hau, sai da gabansa ya fadi ganin tsayin gun da xa su dira, ganin bata lkci yake yi ya juya ya kalli Sadeeq dake jira ya tafi, Sadeeq yace "Just close ur eyes guy ka dira they re almost here," kawai Abuturrab yyi shahada ya dira, Sadeeq ya hau shi ma ya dira, da kyar Abuturrab ya iya mikewa jin kafarsa kmr ba tasa ba bai gama recovering ba kawai sai ganin soldiers kusan hudu yyi alamar gadin gun suke, Sadeeq ya xaro ido yace "Nooo noo, am nt ready for this" Ae Abuturrab mancewa yyi da ciwon kafar ya mike a tare suka yi gabas a 260 wnn karan, Soldiers din suka bi su, Jin karan Harbi ya kara rikita Abuturrab, suna shan kwana sadeeq ya banke gate din wani gida dake kan kwanan gate din ya bude ya fixgo Abuturrab suka shige ya datse gate din, wata yarinya ce ke wanke wanke tsakar gidan ta mike a tsorace tana kallonsu, Sadeeq ya daura hannunsa a lips dinsa yace "Shiii, sojoji ne anguwar, mu suka biyo, Fakewa kawai xa muyi na wani lkci ko bakya taimako...." ita dai kallonsu kawai take, bubbuga gate din suka ji ana yi, Sadeeq ya kalli gate din da sauri, nufar yarinyar yyi yace "In kika rufa mana asiri Allah xae rufe naki" daga haka ya ja hannun Abuturrab suka yi bayan gidan da gudu, yarinyar ta karasa gate din da sauri sai dai duk a tsorace take ta bude, tambayarta sojoji biyu suka yi ko an shigo masu gida, ta girgixa kai tace "A'a" kallom compound din suka dinga yi daga haka suka bata hakuri suka juya ta rufe gate din. Da kyar Abuturrab ya iya magana bayan kusan minti goma yace "Ina take ita?" Sadeeq na share xufar fuskarsa yace "Gun wasu couple a hotel din na kai ta kuma nasa ta shiga bathroom" Abuturrab ya xaro ido yace "Baka tunanin xa su iya shiga duk dakunan suna neman mu?" Sadeeq yace "Haba dai ai tana bathroom, kuma nace kar ta fito, kaga ko da an shiga dakin aka ga mata yara da miji ae wucewa xa su yi" Abuturrab ya jingina jikin bango ya lumshe ido, shi kam tunda ya hadu da Samha komai ya canxa masa a rayuwa, amma kullum karuwa sonta yake a xuciyarsa, Yarinyar suka gani a kansu tace "Ku rufa min asiri ku wuce kafin mamata ta dawo don Allah" Abuturrab yyi shiru, Sadeeq ya d'an yi tsaki ya mike, katangar gidan ya kalla yaga bbu wani tsayi, ya hau Katangar yana lekan waje yaga bola ce, kallon Abuturrab yyi yace "Mu je guy..." Daga haka ya dira kasa, Abuturrab ya kalleta yace "Mun gode" daga haka ya hau shima ya dira, tafiya suke har suka iso express, Abuturrab yace "Sadeeq we need to get her out of the hotel too" kamar ynda Sadeeq yace haka kuwa aka yi, don daki daki soldiers din suka dinga bi sae dae in xa su fita su ba occupant din dakin hakuri, ko xuwa kan dakin da Samha take basu yi ba aka ga fitansu ta baya hakan yasa aka dakatar da search din, Mahaifin Sadeeq da Abuturrab dake tsaye haraban hotel din mamaki ne ya cika su ganin hanyar da suka bi suka fita, Dad din Abuturrab yyi shiru a xuciyarsa kuwa tunanin lkcn da Aliyu ya dawo tantiri haka gaba daya yake, wai ace har yau ya kasa kamasa, can ya girgixa kai yace "This is just getting out of hand, in har Aliyu ya shigo hannuna sai yyi xaman shekara daya a kiri kiri kafin in fara masa hukunci" Abban Sadeeq kam kasa cewa komai yyi, haka dai suka ba ma'aikatan hotel din da manager hakuri suka fita. Mata da miji dai sai kallon kallo suke barin da suka ga Samha shiru bata fito ba, matar ta fara masifa tana cewa "Wai ace kana matsayin mai gida wani ya shigo mana daki haka kawai ka bi sa da ido har ya fita ka kasa cewa uffan, to ni dai bbu ruwana ga yarinya har ynxu bata fito ba in ma mutuwa tayi kai ne a ciki wllh bbu ruwana...." Mikewa yyi ya nufi bayin ya kwankwasa kofa, Samha dake jingine jikin bango tayi mugun tsorata ta kasa cewa komai, matar ta mike ta tura kofar, kallonsu take haka su ma, Mutumin yace "Lafiya baki fito ba yarinya" Samha ta sunkuyar da kai ta bi ta gefensa ta fito ya bi ta da ido, Wani harara matar ta watsa masa ta koma ta xauna kusa da yaranta. Abuturrab yace "Wani room din ka kai ta?" Sadeeq yace "Ni ban kalli number dakin ba" Abuturrab ya shafa kansa yace "How re we going to do this now?" Sadeeq ya d'an yi shiru sai kuma yace "Kasan me, just ka nemi waje ka jira ni, let me go get her out trust me" Abuturrab da yanxu kam ya gama sara ma kitabar Sadeeq kawai yace masa "Alryt" Wani shago ya samu ya xauna Sadeeq ya nufi hotel din. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 55...... Har Sadeeq ya isa hotel din tunanin yanda xai shiga bbu investigation ya fito da Samha yake, can dai yyi deciding yayi pretend kmr lodging ya xo yi, biyan kudin daki yyi ta atm card dinsa ya haura sama, direct ya nufi dakin da Samha take yayi sallama sai da aka amsa ya shiga, Nan yyi masu Godiya yana kallon Samha dake xaune yace "Toh mu je sis" mikewa Samha tayi ta kalli matar tayi mata godiya ita ma snn suka fita, Abuturrab na hangosu ya mike yana kallon Samha ganin yanda ta kara ramewa, suka karaso inda yake, Sadeeq yace "I think it's no longer safe here, Zaria will be a peaceful place to stay!" Abuturrab bai ce komai ba sai dai yasan gaskiya ya fadi, kamo hannunta yyi yace "How re u feeling now?" A hankali tace "Da sauki..." wayarsa ne ya shiga ring ya ciro ya d'aga ya kai kunne ganin mijin Anty Maryam ne, daga daya bangaren yace "Aliyu ka taho gun mai anguwa nan da awa biyu...." Abuturrab yace "Ban san gun ba ai" Mijin Anty Maryam yace "Mai machine xaka fadi ma xae kawo ka, sai ka taho da kudin sadaki ka dai gane?" Abuturrab bai san lkcn da yyi murmushi ba yace "Toh nagode" kallon Sadeeq yayi yace "Guy i know no one in Zaria!" Sadeeq yace "Amm, then sai mu kai ta gidansu babe dina ta tsaya for the mean time...." Abuturrab yace "Is she staying on her own?" Sadeeq yace "Noo wif her parent, kawai dai iyayenta yan boko ne wayayyu kamar mu they re nt like our parents, normal ne a wajensu beside cewa xata yi kawarta ce ae.." Ya kare maganar yana d'aga kafada, Abuturrab yyi murmushi yana gyada kai, can ya kalli Samha ganin mode dinta sai bai ce komai ba amma jikinsa yyi sanyi sosai, kallon Sadeeq yayi yace "Alryt plss ka sama mana mota frnd sai mu je can" Sadeeq yace "Good... But ni baxan jima can ba ina da aiki da xan yi Government house yau" Abuturrab yace "You re really a frnd in need" yar dariya Sadeeq yyi yace "That's me" daga haka ya nufi titi don sama masu abun hawa da xa su Zaria, Abuturrab ya kama hannunta suka koma inda yake xaune ya xauna da damuwa yace "Samha what's wrong...." Kamar jira take ta fashe masa da kuka a hankali, tausayinta yaji sosai, ya jawota jikinsa cikin sanyin murya yace "Am sorry Love, am making you past through all this difficulties, baxan iya rayuwa ba ke bane Samha in har ba haka na dinga yi ba xa a rabani da ke, nafi son ko da xa a rabamu ya kasance ke matata ce komai xai fi xuwa da sauki, i can't just imagine me idan aka yi parting dina da ke Samha, you now a part of me, you transformed me frm who i was then" Bata ce komai ba sai kukan da take a hankali, ya dago kanta yana kallon kyakkyawar fuskarta ya shiga share mata hawayen da ke saukowa idonta a hankali, daure fuska yyi yace "Alryt you stop those tears now idan ba haka ba i give u a french kiss in public...." Kalle kallen wajen ta shiga yi taga ai fa da mutane kawai ta shiga share idonta a hankali, murmushinsa mai kyau yyi ya hade hannuwansu yace "I love you Samha...." Sunkuyar da kanta tayi kasa, ya langwabar da kai cikin sanyin murya yace "No reply wife?" D'an murmushi tayi wanda hakan yasa yaji dadi har cikin ransa don har ya mance rabon da yaga murmushinta, ya murxa hannunta yace "Uhnn?" A hankali ta matsa daga kusa da shi ganin Sadeeq na xuwa, yana karasowa yace "Yeah, Romeo, Juliet ga mota me kyau na sama mana..." Mikewa Abuturrab yyi yana shafa kai suka bi bayansa, har suka isa Zaria kallon agogo yake don bai son ya wuce awa biyun da aka ce masa, tsayawa yyi a wani mall ya d'an yi mata siyayyar abubuwan da yasan xata bukata da drugs snn suka dau hanyar gidansu Zainab budurwar Sadeeq, yar masu kudi ce sosai itama, tun a waya ya kirata ya gaya mata gasu nn xuwa, suna isa gidan ya sanar da ita tafito, yar kyakkyawa da ita ta karaso tana kallonsu da fara'a dauke fuskarta suka gaisa, can ta dawo kusa da Sadeeq tace "Ita ce yarinyar koh?" Yace "Yeah sweet, sauri muke ynxu, xuwa yamma xan dawo" kama hannun Samha tayi tace "Welcome pretty" murmushi Samha tayi mata a hankali tace "Thank you" ita ta karbi ledar da Abuturrab ke mika ma Samha sannan tayi masu sallama Sadeeq ya kashe mata ido yace "Mu yi waya" tayi yar dariya suka wuce ciki tare da Samha. Bbu bata lkci su Abuturrab suka juya, Throughout journey din Abuturrab labarinsa da Samha yake ba Sadeeq dake ta hail dinsa kace abun arxiki yayi, jin a ranan ma xa a daura auren nasu yace "Bravo jare, toh amma shine bbu gayyata gun daurin auren?" Abuturrab yace "Naji kace min kana da aiki a government house" Sadeeq ya sosa kai yace "Yea xa mu je taro governor ne" Abuturrab yace "Are you a soldier also?" Sadeeq ya yamutsa fuska yace "I dodge that!" Abuturrab yace "That funny, you re related to d governor knn?" Sadeeq yace "Inaaa karere fa kawai, son dinsa is my best frnd shine xan rakasa dauko Abban nasa....." Abuturrab yyi dariya yace "Buh what did you study in schl?" Sadeeq ya gyara xama yace "Chemical Engineering, ina aiki a port Harcourt, na dau transfer na koma lagos naga duk shirme ne lagos din, kawai na dawo kd ynxu... Gombe daurin auren wani abokin frnd dina naje suka bata min rai kawai na biyo motar haya ko sani basu yi ba...." Abuturrab da ya saki baki yana kallonsa yace "Uhm that's nyc, where did you schl?" Sadeeq ya d'an yi shiru yana shafa sajensa, sai kuma yace "I always never want to talk about this because i schl in Abuja when my mate are schooling abroad!!!" dariya ssai Abuturrab yyi yace "Why is that" Sadeeq ya buda ido yace "Wai kar in xama terror in ji Abba" Abuturrab bai kuma cewa komai ba sae dai danne dariyarsa kawai yake, can dai yace "Toh ynxu xa ku je taro governor din ne?" Sadeeq yace "A'a bari kawai inje in shaida daurin auren new frnd" Abuturrab yyi murmushi yace "Alryt am grateful" Sadeeq yace "Yanxu dai ni bari in karasa kd sai in samo mana fararen shaddodi ko ya kaga" Dariya Abuturrab yyi bai ce komai ba, Sadeeq yace "Rubuta min number ka xan kira idan na taho, coz kunna waya ba tawa bace ynxu, i will get a frnds phone" gun driver suka karbi pen Abuturrab ya rubuta masa number snn ya basa Atm dinsa yace "Sai ka ciro min 100k sadakin da xan bada" daga haka ya rubuta masa pin din a bayan numbersa, Sadeeq ya karbi takardar yace "Don't worry gudunmawata knn, xan biya maka bride price din" Abuturrab ya buda ido sai kuma yyi dariya yyi patting shoulder dinsa yace "Allah bar mu" Sadeeq ya sosa kai yace "Kuma ya shirye mu" Abuturrab na dariya yace "Yeah, yeah" daga haka ya sauka a maraba mai motar ya wuce da Sadeeq. Abuturrab na sauka ya kalli agogonsa yaga daya saura hakan yasa ya nufi masallaci don yi azahar, wani gun me shago ya zauna bayan ya fito yana jiran Sadeeq, sai kusan biyu sadeeq ya kirasa yace Yana bakin titi shi yana ina, fitowa Abuturrab yyi suka hadu, Sadeeq yace "We need to get a hotel don ka shirya" hotel dake nan kusa suka nufa, Abuturrab na gama shiryawa ya kira Mijin Anty Maryam ya sanar da shi xae taho snn suka dau machine xuwa gidan mai gari. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 56..... Suna isa gidan mai gari suka sauka a dai dai kofar gida Abuturrab na kare ma gun kallo ya fiddo dari biyar dake aljihunsa ya mika ma masu machine din, tuni Sadeeq ya nufi tabarmar dake shimfide kofar gidan da mutane a kai, Abuturrab ya bi bayansa, sai a sannan ya ga mijin Anty Maryam xaune cikin mutanen, kallo daya yyi masu ya gano waye mai garin ganin irin shigar da yayi, Sadeeq ya xauna kan tabarmar ya gaida su gaba daya, Abuturrab ma ya xauna duk ya gaishesu, mai gari ne yayi gyaran murya yace "Toh da wa xa a daura auren cikinsu?" Mijin Anty Maryam ya nuna masa Abuturrab, Mai gari yace "Ya sunansa?" Nan ma mijin Anty Maryam ne ya bada amsa, mai gari yace "Maa sha Allah, Malam Aminu yyi min bayanin komai Aliyu, na kuma ji tausayin ku ainun, amma ina son ka sani in har aka daura auren nn ka cuce yarinyar nn ko ka ci amanarta ko da so daya ne tamkar ka ci amanar musulunci ne, albarkacin islama kayi kkrin ganin ka rike ta da amana Aliyu, abu na biyu kada ka tilastata kace sae tayi addinin ka, ka bari tayi hakan don kanta, kai dai yi iyakar kkrin ka wajen nuna mata shi fa musulunci addini ne mai sauki, halayyanka gareta da irin xamantakewar da xaka yi da ita shi xae nuna mata hakan ba sai ka fito baro baro ka dinga fada mata ba, duk da addinin ku ya sha bam bam ta yrda ta baro iyayenta ta biyo ka don haka in dai ka cuceta ko dai dai da rana daya to Allah xae mata sakayya, ita kuma Allah ya mata rahama ta gane menene musulunci har tayi sha'awar dawowa cikinmu, ni xan xama waliyyinka in shaa Allah, shi kuma Malam Aminu xae xama nata, mun kuma yanke sadakinta a kan dubu hamsin....." Duk jikin Abuturrab yyi sanyi hakan yasa bai iya dagowa ya kallesu ba, Maminsa ce ta fado masa, to haka xa a daura masa aure mahaifiyarsa bata sani ba bare ta sa masa albarka, irin ynda mami ta ci buri kan aurensa ace xa ayi sa ynxu bata sani ba, tunanin hakan ya sakko masa da mugun sanyin jiki duk yaga gaba daya bai kyauta mata ba, Sadeeq ne ya kirgo dubu Hamsin kmr jira yake ya ajiye masu, nan take aka daura auren Aliyu da Samha akan sadakin da aka bayar, har lkcn Abuturrab bai iya ya dago kansa da yaji yyi masa nauyi ba, Malam Aminu ya jawo ledan goronsa da alawa ya bude ya shiga rarrabawa mutanen dake xaune gun ana ta sa ma auren albarka, ganin Shirun Abuturrab yyi yawa Sadeeq ya tabo sa sai a snn ya dago da sauri, Murmushi ya kirkira cikin sanyin murya yace "Allah ya ba ni ikon riketa a bisa koyarwar addinina ya kuma taya ni fahimtar da ita gaskiya da wuri..." Duk aka amsa masa da Ameeen, basu wani jima ba suka mike gaba daya har da Malam Aminu suka yi ma mai gari da sauran mutanen gun godiya snn suka wuce, Malam Aminu yace "Yanxu xa ku je can gun Antyn tata tana son ganinku wai, amma ba gida xa ku sameta ba, sae mu je in raka ku inda xa ku sameta" har suka isa gidan Malam Aminu nasiha yake ma Abuturrab kan kada ya bari Samha tayi da ta sanin amincewa da shi, ya dinga nuna masa kada ya manta ita kadai ke gare iyayenta bbu irin jin ddin da ba a shayar da ita ba a rayuwa bbu gatan da bata samu ba tun daga kan iyayen nata har kan yan uwa, amma lkci daya ta yrda ta amince da shi ta guji kowa nata ta biyosa, kada ya bari wataran maganganun da mahaifiyarta ke yawan yi na cewa ae musulmai basu da alkawari basu da amana ya xamto gaskiya ya nuna karya take bbu abinda ya kai musulunci gaskiya da rikon amana, ya nuna mata musulunci Rahama ne, Abuturrab bai iya yace masa komai ba kansa a kasa, sae Sadeeq dake ta cewa wnn gaskiya ne, xaune suka tadda Anty Maryam tsakar gidan uwar dakinta bayan an masu ixinin shigowa, nn dai malam Aminu yyi masu sallama don xae koma gun harkokinsa ya bar su daga su sai Anty Maryam da uwar dakinta Hajiya Salamatu, cikin sanyin murya Anty Maryam tace "Aliyu kai musulmi ne ni musulma ce, mun san Do's and don't din addininmu, don't let my daughter regret trusting a musulim, make her fall for it plss, show her it's teaching and aim, Samantha ita kadae ke gare yayana don't ruin her life, idan ka ci amanarta tamkar ka ci amanar addininmu ne...." Tana magana ne hawaye cike idonta, Abuturrab ya kasa kallonta, Hajiya Salamatu tace "Ina jin ta fada maka duk abinda ya kamata D'an nan, kar ka ba mu kunya ka rike amana, Allah kuma ya kawo sassauci cikin lamarin ya huci xuciyar iyayenku, sae kaga ta dalilin hakan Allahu ya dawo da iyayenta hanya madaidaiciya, ita kuma ina mata fatan amsan kalmar Shahada nan ba da ddewa ba, sae dai hakan xae faru ne idan ka rike a bisa koyarwar Musulunci sae kaga don kanta hakan ya burgeta..." A hankali Abuturrab yace "In shaa Allah" Anty Maryam tace "To yanxu kuma ina ku ka nufa?" Abuturrab ya d'an shiru sai kuma yace "Kila mu koma Gombe can ya fi kwanciyar hankali Anty" Cikin sanyin murya Anty Maryam tace "Toh Allah yasa hakan da alkhairi, idan Babansu Asiya ya yrda sae in bi ku in ga inda ku ke...." Ya d'an yi murnushi yace "Toh Allah yasa ya yrda Anty" Hajiya Salamatu tace "Toh yanxu ina ita Rebeccan take?" Abuturrab yace "Zaria muka kai ta da abokina" Anty Maryam tace "Gun wa a Zaria?" Abuturrab yace "Gidansu yarinyar da xae aura yasa muka kai ta" Murmushi kawai Sadeeq yyi, Hajiya Salamatu tace "Toh dama ina son ita ma mu xauna da ita ne, sae dai kuma dawowanta nn da hatsari sosai, kanwata na Zaria ko gobe sae mu je can da Maryam ku kai mana ita gidan kanwar tawa" Abuturrab yace "Toh Allah ya kai mu" Anty Maryam tace "Shknn Aliyu Allah ubangiji ya hada kan ku ya baka ikon rikon amana, xa ku iya tafiya" Sadeeq ne yyi masu godiya snn Abuturrab, duk suka mike Sadeeq ya ciro sauran dubu hamsin din ya ajiye gabansu yace "Ga wannan bbu yawa Anty..." Bbu ynda Anty Maryam da Hajiya Salamatu basu yi ba kan su tafi da kudinsu amma basu dauka ba suka fita, samun Machine bai masu wahala ba a kofar gidan, suna isa titi Sadeeq yace "Ya ne frnd na ga mood dinka ya canxa, you ought to be happy ta xama mallakin ka yanxu ae" Cikin sanyin Murya Abuturrab yace "Sadeeq my mum knew nothing about this, kaga bn fita hakkinta ba, bn mata adalci ba, am just restless" daga haka ya nemi gu ya xauna ya rike kansa, Sadeeq ya durkusa gabansa yace "And that's very through, kana bukatar addu'anta, kana bukatar ta sa maka albarka" Dago kai Abuturrab yyi lkci daya idonsa ya kada ya kasa cewa komai, Sadeeq yace "Here is an advice, why not ka je kano, you do all you can ku hadu da ita secretly sae kayi mata bayanin komai, uwa ce xata fahimce ka...." Shiru Abuturrab yyi sae kuma ya gyada kai yace "Yea, gaskiya hakan xan yi frnd, xan je gidan sister dinta, sae mu hadu a can in shaa Allah, buh if you're less busy plss mu je tare" Sadeeq ya shafa kansa bai ce komai ba, sae kuma can yace "Alryt ba damuwa mu je frnd..." Abuturrab ya mike yace "That's kind of you" Sadeeq yace "Za mu fara xuwa Zaria kenan?" Abuturrab yace "Noo, mu tafi kanon kawai, but before then i need to change" Boutique suka nufa suka siya kananun kaya da P cap snn suka koma hotel din da suka yi lodge, suna gama shiryawa suka fito suka samu mota xuwa kano. Sai kusan karfe uku da rabi suka shigo kano, suna fitowa daga park Abuturrab yasa p cap dinsa yanda in dai ba durkusawa kayi ba to ba lallai ka ga fuskarsa ba, Sadeeq yyi dariya yace "Saboda tsaro ba don tsoro ba koh?" Dariya Abuturrab yyi shi ma yace "Sure kai ma daura naka" Sadeeq ya daura cap din shi ma, adai daita sahu suka dauka da xae kai su har Nasarrawa, basu suka isa gidan Hajiya Mariya ba sae kusan Hudu da rabi, suka sauka a sahun suka basa kudinsa, lkci daya gaban Abuturrab ya shiga faduwa, daga cikin p cap din ya dinga surveying anguwar kafin ya kwankwasa gate mai gadi ya bude masu, ya daga hular kansa suka gaisa ya mayar snn suka shiga gidan da Sadeeq. Babban parlon Small Mum din tasa ya nufa mai aiki ta bude masu kofa bayan sun danna bell suka shiga parlon suka xauna, ta wuce sama don kiran Hajiya Mariya, Abuturrab ya kalli Sadeeq yace "Kasan me?" Sadeeq ya girgixa masa kai, a hankali yace "I'm just restless" Sadeeq yace "Chill, bbu abinda xae faru in shaa Allah, mu da muka san Allah na tare da mu...." Saukowar Hajiya Mariya yasa yyi shiru, ta karaso parlon tana kallonsu gaba daya duk da ba ganin fuskarsa take ba amma ta gane Abuturrab ne, shi kam ya ki kallon inda take har sae da ta iso gabansa, a hankali tace "Aliyuuu" dago kai yyi ya cire cap din kansa, kasa boye farin cikinta tayi, ya mike ya rungumeta yana murmushi yace "Sweeet Mum" dago kansa tayi lkci daya farin cikin yyi fading ganin yanda ya rame ba kadan ba sai haskensa dake nn kawae, shafa kansa tayi cikin sanyin murya tace "Daga ina kake Aliyu!" Komawa baya yyi ya nuna mata Sadeeq yace "Meet my frnd, a brother!" *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 57..... Kallon Sadeeq Hajiya Mariya tayi, can tayi murmushi ta nufesa shi ma tace "Welcome Son! Kai ne d'an wajen Col Ishaq koh?" Sadeeq yayi kasa da kai ya gaisheta ta amsa har lkcn murmushi dauke fuskarta, can ta kalli Abuturrab tace "Aliyu daga ina ku ke?" Ya d'an shafa kai a hankali yace "Kaduna Mum" dawowa tayi kusa da shi ta xauna da damuwa tace "Aliyu ina yarinyar take?" Yace "Mum tana kaduna" Shiru tayi tana kallonsa, can ta mike ta nufi fridge ta dauko masu ruwa da drink ta ajiye masu, kamar Abuturrab jira yake ya dau exotic drink din ya bude ya kai baki ya sha iya wanda xai sha ya ajiye sauran, Hajiya Mariya sai kallonsa take, jingina yyi jikinta cikin sanyin murya yace "Mum Mamina fa?" Hajiya Mariya ltayi shiru har sai da ya kalleta snn tace "Tana gida Aliyu, fushi take da kai..." da sauri yace "Plss ki kirata ta xo nan momma, i came because of her...." Ta girgixa kai tace "I don't think xata yrda ta xo, beside i guess Abban ka na gida yanxu haka" da damuwa yace "Plss Mum ki lallaba min ita ta xo in ganta ko xan ji dadi" Hajiya Mariya bata ce komai ba, can tace "Toh ita yarinyar gun wa ka bar ta?" Yace "Sun hadu da aunt dinta" Hajiya Mariya ta buda ido tace "Haba, sai aka yi ya kenan?" Ya langwabar da kai yace "Musulma ce aunt din, Mijinta kuma ya bani shawarar aurenta kawai, daxu aka daura auren ma..." mikewa Hajiya Mariya tayi tana kallonsa da mamaki tace "Aliyuu" A sanyaye yace "I have no option mum, and... I love her, shi yasa na taho gun mami i shud ask for forgiveness, i know i wronged you all, but ba laifina bane Mumy" rike kansa yyi ya lumshe ido, Hajiya Mariya bata kuma cewa komai ba ya sakko kasa a hankali on his kneels yace "Pls ki kira min ita mum..." Hajiya Mariya ta xauna gefen kujera tayi tagumi bata ce komai ba, Sadeeq ya lumshe ido ya bude yace "Mumy plsss ayi hakuri for the sake of islam..." Bata kuma cewa komai ba ta mike ta nufi daki, Sadeeq ya kallesa yace "Chill Guy xata kira mana ita in shaa Allah" Hajiya Mariya na isa bedroom dinta ta dau wayarta ta xauna gefen gado tayi dialing number yayarta ta kai wayar kunne, Mami dake dakin Abban Abuturrab tana gyara masa press dinsa shi kuma yana xaune dakin kan resting chair idonsa sanye da glass yana duba newspaper din ranan da bai samu ya duba ba, kallon wayarta dake ajiye gefen gado tayi jin yana ring, ta isa gun wayar ta dauka, ganin Mariya ce ta daga ta kai kunne hadde da sallama, daga daya bangaren Hajiya Mariya tace "Ina yini yaya?" Mami tace "Lafiya Mariya ya gidan?" Hajiya Mariya tace "Alhmdllh, ya su Ramla?" Mami tace "Lafiya lau su ke, sun je Saloon" Hajiya Mariya ta d'an yi shiru har sai da Mami tace "Hello!" Snn a hankali tace "Yaya Aliyu na nan gida na, idan Col bai gida ki daure ki taho don Allah" Mami bata san lkcn da ta xauna gefen gado ba lkci daya duk tayi sanyi ta kasa cewa komai, Abba dai kallonta kawai yake ta gefen idonsa dake cikin glass yana lura da ita, Jin shirun da Mami tayi yasa cikin sanyin murya Hajiya Mariya tace "Kinyi shiru yaya" Mami ta saci kallon Abba da yayi saurin dauke idonsa ya mayar kan newspaper din hannunsa, Katse wayar tayi ta ajiye, a hankali tace "Ba jin ki nake ba Mariya" mikewa tayi ta ci gaba da abinda take sai dai da ganinta kasan hankalinta bai ma kan abinda take, kallonta kawai Abba yake ta glass, Hajiya Mariya ta kalli wayarta jin yayarta ta katse, duk jikinta yyi sanyi ta kuma dialing number, juyowa Mami tayi da sauri jin karan wayar kuma, suka hada ido da Abba ta karasa ta dauka ta kai kunne tace "Mariya ba jin ki nake ba ki bari anjima ki kira, the network is fluctuating" daga haka ta katse wayar ta ci gaba da abinda take, tana gamawa ta dau wayarta tace "Yallabai bari in je a fara shirin girkin Dinner!" Ba tare da ya kalleta ba yace "Ok" daga haka ta nufi kofa ya bi ta da ido har ta fita. Mami na isa dakinta ta kulle kofa ta shiga kiran kanwar tata, Hajiya Mariya dake xuba ma su Aliyu abinci ta mike ta dau wayarta jin ringing, tana ganin yayarta ce ta daga da sauri ta nufi daki, Mami tace "Mariya kika ce Aliyu na gidan ki?" Tace "Ehh yaya, ki daure ki taho don Allah...." Mami tayi shiru, sai kuma cikin sanyin murya tace "Col na gida" Hajiya Mariya ta buda ido tace "Toh to ki bari kar ki xo yaya, ko xuwa gobe sai ki samu inda kika ce masa xa ki, nasan xa su kwana ne ma" Mami da taji kamar ko yanxu Aliyu na iya disappear kuma ta girgixa kai da sauri tace "Xan san yanda na fito Mariya..." Daga haka ta katse wayar, rasa abun yi tayi, ta kusa minti biyar a tsaye kafin ta fita, dakin mai gidan nata ta nufa ta gansa tsaye kusa da window waya kare kunnensa, Bai cire wayar ba sae dai ba magana yake ba har ta karaso tace "Yallabai na mance ban gaya maka nama ya kare ba balle a kawo wani, ynxu ko wanda xa ayi amfani da ma bbu" Ya katse wayar kunnensa yace "Toh yanxu ya xa ayi?" Tace "Fita xan yi da mota kawai in siyo wanda xa ayi amfani da, tunda yaran basa nan kuma driver na can tare da su" Abba ya daga kafada yace "If that's ok by you, ga Atm can, sai ki siyo har na amfanin gobe, idan ya so xuwa jibi sae a kawo maku" Tace "Toh shknn, ko xa mu je tare?" Girgixa kai yyi yace "Xan yi bak'i, ki dai siyo min Ginger powder for tea" tace "Alryt" daga haka ta nufi kofa, yace "Atm card din fah" ba tare da ta kallesa ba tace "Akwai cash hannuna" bin ta yyi da ido har ta fita dakin, Makullin mota kawai ta dauka a dakin ta bayan ta saka hijab ta fita ta dau mota ta bar gidan, ta window Abba ke kallonta har ta kure masa, d'an murmushi Abba yyi ya sake curtain din. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By Khaleesat Haiydar📚✍🏻 58..... A hankali Mami ke driving din, gaba daya ta rasa dalilin da yasa hankalinta ya ki kwanciya tun da ta bar gida, parking tayi ta kafa ma steering ido kamar me naxari, but it's very unusual tace ma Col xata fita lkci daya ya bar ta, sannan shi mutum ne da bai son sae abu ya kare a gaya masa sae gashi yau ko canza fuska bai yi ba, girgixa kai tayi ta dau wayarta ta shiga kiran Hajiya Mariya, tana dauka cikin sanyin murya tace "Mariya, ina tunanin Col ya gano ni, tun da na fito gida hankalina ya ki kwanciya kuma yasan kin kira ni, Aliyu ya bar gidan ki, but make him promise baxai tafi ba, don Allah kar ya tafi" Hajiya Mariya da hankalinta ya tashi ita ma tace "Toh yaya nasan baxae tafi ba baku hadu ba...." Daga haka ta katse wayar ta fito parlor da sauri tana kallon Abuturrab tace "Aliyu, Mami ta kira yanxu, it seems Abba ya gano kiran da nayi mata, you two have to leave now immediately...." Ko rufe baki bata yi ba Abuturrab ya mike kamar wanda aka tsikara haka ma Sadeeq, Hajiya Mariya tace "Amma don Allah don Annabi Aliyu kar ku wuce, make that promise to me son!" Cap dinsa ya dauka yace "Baxan tafi ban ga Mami ba ae, xa mu yi waya mum" daga haka ya ja hannun Sadeeq suka fice, ta bi su da ido a sanyaye, Abuturrab bai yrda sun bi main road ba suka canxa hanya daga shi har Sadeeq din a dar suke, basu xarce ko ina ba sae wani local hotel. Mami na kiran Hajiya Mariya dama kasuwa kawai ta wuce ta siya abinda xata siya, bata yi mamakin rashin ganin mai gidan nata a gida ba, da yake su Ramla sun dawo su ta hada da girkin tunda masu girkin basa nan ta wuce dakinta kawai. Ko minti sha biyar ba ayi da fitansu Aliyu ba mai gadi ya xo yana bubbuga kofa, Hajiya Mariya da ta xauna ta rafka tagumi a parlon ta mike da sauri ta dau hijab ta sa ta isa kofar ta bude, ganin yanayin mai gadin tace "Lafiya Sulaiman?" Yace "Hajiya ba lafiya ba, sojoji ne birjik bakin gate wai kuma gidan nan suka xo xa su shiga...." Nan da nan Hajiya Mariya ta hade rai tace "Sai kace masu me?" Yace "Ban samu damar magana ba ni dai na yo nan a guje...." Tsit yyi ganin Sojojin sun shigo suna tahowa Balcony, wasu kuma sun xaga baya, wasu na tsaye daga gate, Hajiya Mariya ta wani murtuke fuska ganin Abban Abuturrab don shi ne ma gaba, gabanta ya isa yace "Ki ban number mai gidan ki mun shigo masa gida ba izini..." Tace "Ko me ya janyo hakan?" Yace "Za ki sani nan ba da dadewa ba, basu hanya su shiga...." Ta girgixa kai tace "Babu wannan xancen Abban Ramla, ya xa ku shigo min gida haka ina matsayin matar aure mai gidana bai nan, wannan ko ni nace Aliyu ya bar gida da yar mutane sai haka ai, ni wllh ina ganin mutuncin ka a matsayin ka na mijin yayata banda haka bbu abinda xai sa na ci gaba da daukan wnn cin fuskar haka...." Wayarta ta latsa a fusace ta kira Mami, Mami na dagawa tace "Yaya kiyi hakuri, amma gaskiya bana son wnn abinda Abbansu Ramla ke min, duk fadin kano ya rasa warce xae dinga xargi kan barin Aliyu gida sae ni, a kan wani dalili xae kwaso min bariki guda na soldiers ya shigo min gida ko mai gidana bai sani ba...." Mami dai na sauraranta bata ce komai ba sai dai ita ma gaba daya ranta yyi mugun baci, katse wayar tayi tace "Toh sai ku shiga ku fiddo Aliyu...." Daga haka ta fice fuu ta bar masu gidan gaba daya. Hakan bai hana Abba yasa an duba masa gidan ciki da bai ba amma bbu Aliyu bbu alamarsa. Sae bayan Magrib ya koma gida, har lkcn kuma xuciyarsa ta kasa yrda cewar Aliyu bai je gidan Hajiya Mariya ba, har karfe tara Mami bata je part dinsa ba, abinci ma su Ramla tasa suka kai masa, tun da suke bata taba yi masa irin haka ba, da yaso sharewa amma kawai ya tashi ya tafi can dakin nata, tsaye yyi bakin kofa yace "Hajarah baki ji dawowata bane?" Tace "Gaskiya, don na bada tare da Aliyu xa ku dawo gidan nan yau..." D'an murmushi yyi ya juya ya fita daga dakin. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 59..... Bayan magrib Aliyu na kwance Sadeeq ya kira Zainab, basu ji ma suna waya ba yace ta ba Samha wayar, tana mika mata ya kalli Abuturrab ya mika masa wayar yace "Ur wife" mikewa xaune Abuturrab yyi ya karbi wayar, Sadeeq ya mike yace "Let me get us something to eat" daga haka ya fita, Abuturrab ya kalli screen din wayar jin shiru yaga har lkcn ba a katse ba, A hankali yace "Assalamu alaikum" duk da yasan it's wrong, Samha dake xaune dakin tare da Zainab da kanwarta ta sunkuyar da kai bata ce komai, murmushi Zainab tayi ta mike ta fita Hafsat ta bi bayanta, Abuturrab yasan tana jin sa hakan yasa yayi shiru shi ma, jin shirun yasa cikin sanyin murya tace "Ina yini?" Ya langwabar da kai yace "Baki amsa sallama ba wife?" Murmushi tayi kmr yana ganinta tace "Peace be unto you too" ya wara ido yace "That's sweet baby, how you?" Tace "Lafiya lau" yace "But do you like it there?" Gyada masa kai tayi kamar yana ganinta tace "Yeah" yace "How about the cramps?" Tace "Da sauki" d'an shiru yyi kafin yace "Kin ci abinci kuwa" tace "Mun ci yanxu" ya lumshe ido yace "Baby you re now mine" bata ce komai ba don bata ma gane abinda yake nufi ba, yace "An daura auren mu daxu...." Dago kai tayi da sauri tayi shiru, lkci daya mood dinta ya canxa, a hankali yace "Samha!" Nan ma bata ce komai ba, yace "I know you re there" Da kyar ta bude baki tace "ban gane bane" Yace "You are now my wife in shaa Allah" tace "How?" Yar dariya yyi yace "I will explain better idan na xo yarinya" Bata kuma ce masa komai ba, yaso ce mata yana kano amma ya fasa don bai son daga mata hankali, yace "Gobe xan xo idan Allah ya yrda kin ji Babynah" "Toh" kawai tace masa yace "Kin sha drugs din ki?" Tace "Na sha" yace "Good, sleep tight wife, xan inyi isha yanxu" tace "Toh" ya kuma yi mata sai da safe ya katse wayar. Washegari shi ya kira Hajiya Mariya, nan ta gaya masa inda xa su je wato gidan wata kawarta. Karfe goma sha daya suka isa gidan suka tarar har ta je tana jiransu, bayan sun gaisa yake tambayarta Mami fah, tace "Tana hanya, yanxu na kirata, kun karya kuwa?" Ya gyada mata kai yace "Mun yi break Mum" Sai kusan sha biyu Mami ta iso gidan, da yake tun kwanaki biyu da suka wuce tace ma Col xata fita da wnn excuse din ta fito yana bacci ma ta baro gidan, tun da Abuturrab yaji shigowarta gabansa ya shiga faduwa, Sadeeq kam kallonta yake don ya santa years back, ta karaso parlorn tana kallon Abuturrab fuska daure, ba tare da ya kalleta ba ya mike tsaye duk jikinsa yyi sanyi sosai, karasawa yayi gabanta ya rungumeta, duk yanda ta so hanasa yin hakan kasawa tayi, ji tayi duk wani bakin ciki da ta shiga a baya tun barinsa gida ya gushe lkci daya a xuciyarta jin d'an nata a jikinta, a hankali tayi karfin halin janyesa jikinta, ya durkusa kan kneels dinsa ya hade kansa da kafafuwanta yace "Forgive me Mami, i know i failed you, i disappointed you, i caused you go through a lot...." Tuni hawaye ya kawo idonta ta durkusa gabansa tace "Why did you choose to make me look at fault always, Why Haiydar, me yasa baka san farin ciki na, me yasa baka jin ddi idan baka sa ni cikin matsala one way or the other ba" bai iya ya dago kansa ba, Mikewa Sadeeq yayi ya fice daga parlon don bai ma son ganin scene din sak irin yanda suke da mahaifiyarsa ko da yaushe, Abuturrab kam bai iya ya dago kansa ba jin furucinta, jin hawayensa a kafarta ta dagosa tana kallon fuskarsa, tun bayan tasowarsa yau ce rana ta biyu da ta kuma ganin yana hawaye, ta dake tace "Daga ina kake Aliyu?" Sunkuyar da kansa yayi a hankali yace "Kaduna" Ji tayi kamar ita ma ta fara hawayen ganin irin ramar da yyi, wannan wani irin so ne Aliyu ke ma yarinyar nn har yake neman hallaka kansa, hannunsa ta kamo cikin sanyin murya tace "Ina yarinyar take Ali?" Sai a snn ya kalli kwayar idonta ya ga damuwa karara cikinsu, ya lumshe ido cikin rawar murya yace "Ki yafe min plss Mami, sbda fushin ki gare ni babban masifa ce, na tuba Mami" Mami tace "Ce maka nayi ina yarinyar mutane? Ina ka kai ta?" Ita kam Hajiya Mariya tagumi tayi haka kawarta dake xaune tana kallonsu, Abuturrab ya kalli small mum din tasa snn ya sunkuyar da kai cikin sanyin murya yace "Tana kaduna Mami" Mami ta dago kansa tana kallonsa tace "Toh in har na isa da kai ka koma yanxu ka maidota!" Ya daura fuskarsa a kanta hawaye na sakko masa cikin sanyin yace "Don Allah kar ki ce min haka Mami, wllh baxan iya rabuwa da ita ba, ki min rai, i can't do without her....." Jikin Mami yyi sanyi ta daga kai tana kallon Hajiya Mariya, Tuni hawaye ya kawo idonta tace "Toh me kke nufi da mu Aliyu, ya kake son mu yi maka, wnn wace masifa ce ta same ka" Da kyar yace "Mami ba masifa bace sonta kawai nake tsakanina da Allah" Mami da hawaye ya shiga sakko mata tace "Waye kke tunanin xai bar ka ka aureta Aliy, Abbanka ko Yakumbo ko kuma iyayenta?" Girgixa mata kai ya shiga yi har lkcn kansa na jikinta a hankali yace "Mami addu'ar ki gare ni xai sa komai ya xo min da sauki, Support me my world" Shiru Mami tayi, hakan yasa ya dago kansa da yayi jajir yana kallonta, tausayin dan nata ba kadan ba ta dinga ji har cikin ranta, wanda hakan yasa hawayenta ya ki tsayawa, Hajiya Mariya mikewa tayi ita ma hawayen idonta ta bar wajen, rungumeta yayi cikin rawar murya yace "Mami ni ban san irin son da nake mata ba....." Shafa kansa Mami tayi tace "Ai so ba hauka bane son, yarinyar nn ba muharramar ka bace amma kke xaune da ita gida daya ka mance koyarwar addinin ka" ya girgixa kai yace "Mami i tried my best ban saba ma ubangijina ba throughout our stay together, kuma Mami...." Kasa karasawa yayi don bai san yanda xata dau xancen ba, ta dago kansa tana kallon kwayar idonsa tace "Kuma me?" Sauke idanuwansa kasa yyi a hankali yace "She's now my wife..." Kallonsa Mami take ko kiftawa bbu, can tayi karfin halin cewa "How?" Cikin sanyin murya yace "Daxu mijin kanwar Abbanta yasa aka daura auren, they re muslims" Mami bata iya tace komai ba sai dai wasu sabbin hawayen ne ke sakko mata, hade kansa ya kuma yi da kafarta shi ma hawayen na sakko masa, da kyar tace "Aliyu har xa a daura maka aure without consent dinmu..." Ya girgixa kai yace "Forgive me mother, i knw i failed you, kar ki yi fushi da ni, I've gone through a lot, kullum hankalina ba kwance yake ba, amma idan kin ce in saketa..." Shiru yayi sai kuma cike da karfin hali yace "Sae in saketa, i won't fail you again, amma nasan da sonta xan bar duniyar nan, Allah ne ya jarabbceni mami, nasan tun tasowata nake sa ku magana amma kinsan Mami tunda nake ko frnds Christian ban son yi, ban taba shigowa gida da nonbeliever ba bana son su, i don't like them, sai gashi lkci daya, i knw jarabawata kenan a duniya...." Hawaye yake sosai, Jikin Mami yayi sanyi sosai ita ma hawayen take tace "Allah yasa hakan shine mafi alkhairi Aliyu, na yafe maka, dama ni baka min komai ba, Allah ubangiji ya hada kanku, ita kuma Allah yayi mata rahama.... Allah ya sassauta lamarin ya huci xuciyar Abban ka" Rungume Mami yayi ya ma rasa abinda xai ce mata, Kawar Hajiya Mariya dake xaune ita ma ta ci nata kukan tana murmushi tace "Toh yaushe xa a kawo mana amaryar Ali" Kallonta yyi, yyi murmushin karfin hali yace "Idan Allah ya yrda" Mami na share fuskarta tace "Ku fara shirin barin garin nan yanxu" daga haka ta mike tana kallon Hajiya Farida dake xaune tace "Ki kira min Mariya don Allah" Hajiya Farida tace "Ki shiga tana daki Mami" Dakin Mami ta nufa, Hajiya Farida tace "Allah sanya alkhairi Ali, ka yi kkrin kyautata mata yanda xata yi sha'awar addininmu don kanta, Allah bada xuri'a dayyaba, ya huci xuciyar iyayenku" Bai iya ya dago kansa ba yace "Ameen mum nagode" ba a dau lkci ba Hajiya Mariya suka fito da Mami, Hajiya mariya ta karasa gabansa ta xauna tace "Idan Allah ya yrda xan xo inda ku ke Son, Allah bada xaman lfya, amma kada ka cuceta Ali" sunkuyar da kai yayi bai iya yace komai ba, Balcony Mami ta nufa ta sami Sadeeq xaune, yana ganinta yyi kasa da kai yace "Umma ina yini?" Murmushi tayi tace "kai ma ka ki girma har ynxu ko Abbakar, ka biye wa Aliyu kuna ja ma kanku fitina gun mahaifan ku koh?" Bai dago kai ba illa murmushi da yake yi kawai, tace "Allah ubangiji ya shirya min ku gaba daya..." Sai kusan karfe biyu Abuturrab suka fara shirin barin kano, Mami ta kuma yi masu nasiha sosai ta dau atm card dinta ta basa duk jikinta a sanyaye sai taji kamar kar ya tafi, yaji ddi sosai ya rungumeta, Hajiya Mariya ce ta kai su har Park ta jira sai da motar ya tashi snn ta juya ita ma a sanyaye ta koma gida. *Haske writers asso* Afuwann!! 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 60..... Tunda suka baro kano Abuturrab ke bacci har suka kusa Zaria, Sadeeq kam ya samu wani gaye sai hiran kwallo suke a motar, shi ya tada Abuturrab da suka isa Zaria, bayan sun sauka ya kalli Abuturrab ganin mood dinsa yace "But you ought to be happy frnd kun yi reconciling da Mum fah, why the dullnes" Abuturrab ya d'an yi murmushi yana shafa kansa a hankali yace "Am having headache Sadeeq, it's all stress" Sadeeq yace "Allah ya sauwake, xa mu je can gidansu Zainab ynxu koh?" Kai Abuturrab ya gyada masa, sae da suka yi la'asar snn suka shiga gidan bayan sun isa, har parlor aka yi masu iso, Kanwar Zainab ta kawo masu ruwa da lemo, ba a dau lkci ba mum dinsu ta fito, suka gaisheta da ladabi ta amsa da fara'arta tana masu sannu da xuwa, tana barin parlon Zainab suka fito tare da Samha, tun kan su karaso parlorn Abuturrab ke kallon Samha ko kiftawa bbu, Abaya ce jikinta baki yayi mata kyau ba kadan ba ta daura veil dinsa a kai, d'an wet lip ne kan pinkish lips dinta, ya sauke idonsa kan fingers dinta da aka yi ma jan lalle da ya haska su, duk sai yaga tayi masa kyau ba kadan ba, Gefen Zainab ta xauna ta d'an saci kallonsa ganin kallonta yake tayi kasa da kanta, murmushi dauke fuskarsa ya amsa gaisuwar Zainab, Samha ta kalli Sadeeq cikin sanyin muryarta tace "Ina yini" yyi murmushi yace "lafiya lau, ya ki ke" tace "Lafiya" Abuturrab dake kallon Samha har lkcn yace "Good evening ma'am" murmushi tayi tana wasa da fingers dinta tace "Ina yini" bai amsa ba ya dau glass ya debi ruwa ya fara sha, yana ajiyewa ya kalli Sadeeq yace "Frnd xa mu tafi ynxu ne ko sai ltr" Sadeeq yace "As you wish" Zainab tace "Kar ku ce min yau xa ku wuce min da sabuwar kawata" dariya Sadeeq yyi yace "Sabuwar kawar ki kuma amaryar Abokina ba..." Ta d'an buda ido tace "Toh Allah ya nuna mana lkci" yace "Lkci ya xo har ya wuce ae, matar sa ce fa ko don ban fadi maki ba Soulmate" ta xaro ido tace "Are you kidding?" Ya girgixa kai yana murmushi yace "Am not!" Kallon Samha da taki dago kai tayi, kawai sae tayi murmushi tace "Wlh i taught we re of the same category, Allah sarki, i never knew she's married, Allah bada xaman lafiya" Sadeeq yace "Ameen, kin ga sae ku fara xumunci tun kafin mu yi namu auren koh" dariya tayi haka ma Abuturrab da yace "Toh Allah ya nuna mana" sai kusan karfe biyar suka bar gidan bayan an tilasta su sun ci fried rice da aka xubo masu, dubu goma Abuturrab ya ba sis din Zainab suka rakosu har bakin gate snn suka koma cike da kewar Samha don haka kawai Zainab taji tana burgeta ga ta da kyau sosai da kunya a cewarta. Suna isa titi Sadeeq yace "Frnd xan shiga kd ina da wani appointment... Ku kam dole ku kwana nan tunda Frnd din aunt dinta tace xaka kai masu ita..." Abuturrab yace "Yea, nasan kila they've being tryn calling me gashi na kashe wayar tun daxu" Sadeeq yace "Sae ka kira su ka sanar da su gobe xaka kai masu ita" Abuturrab yace "Alryt frnd" kallon Samha Sadeeq yyi yace "Toh amaryar mu xan koma kaduna, xa mu dinga gaisawa a waya, Allah ya sanya alkhairi...." Murmushi tayi ta sunkuyar da kai tana jujjuya ledan hannunta tace "Allah ya tsare hanya" daga haka Abuturrab ya basa hannu yace "Am soo grateful Abbakar Allah bar mu tare, you re a really a frnd in need, xan shigo kd kafin mu bar garin" Sadeeq yyi murmushi yace "Aiitt, Allah ya kawo ka" daga haka suka rabu Abuturrab ya bi sa da kallo sai yaji kmr kar ya tafi. Napep ya samu yace ya kai su nearest hotel, sai kallon Samha da taki barin su hada ido yake a Adai daitan har suka isa wani hotel me kyau, ya fito snn ita ma ta fito ya ba mai adai daitan kudi, ya kama hannunta da nufin su shiga hotel din ta warce hannunta, bai ce komai ba ya nufi gate din hotel din ta bi bayansa. Yana karbar masu daki aka basa makulli ya bar reception din, ita dai tana biye da shi, babban daki ne mai kyau da makeken gado, ganin tsaye tayi bakin kofa ya juya yana kallonta, taki barin su hada ido, murmushi yayi yace "Yar shariyar ce a kusa baby?" Kin cewa komai tayi ta ki kallonsa kuma har lkcn, bai kuma ce mata komai ba ya kunna Ac yyi kwanciyarsa, ko minti goma bai yi da kwanciya ba bacci ya daukesa, har fa lkcn Samhan ku na tsaye tana kare ma daki kallo, lkci lkci kuma ta kallesa, can dai da taga kmr baccinsa yyi ta karasa dakin ta ajiye ledan kayan hannunta ta xauna can karshen gadon tana satan kallonsa, can ta mike a hankali ta dawo gefensa ta xauna tana kallon fuskarsa, sosai taga ya rame lkci daya jikinta yyi sanyi, ta fi minti ashirin tana xaune wajen kafin ta sauka kasa a hankali ta kwanta kan tiles din dakin, har aka fara kiraye kirayen magrib tana k'asa kwance, jin xa a tada sllh ta mike xaune tana kallonsa, ganin ya juya kansa xuwa daya side din ta mike ta isa kusa da shi a hankali ta durkusa tace "Xa a tada sllh fah doctor" jin baxae taba jin ta ba a haka ta dan tabo hannunsa a hankali, dauke hannunta tayi jin jikinsa da xafi, ta mike ta karasa xuwa daya side din ga mamakinta sai taga idonsa biyu, durkusawa ta kuma yi gabansa da damuwa tace "Are you sick?" Murmushin karfin hali yyi mata a hankali yace "it's just headache dear" xaunawa tayi gefensa kamar xata yi kuka tace "toh baka sha magani ba kuma" mikewa yyi xaune da kyar yace "Xan sha" xata yi magana yayi mata murmushi ya kamo hannunta yace "I will be alryt baby, bari in je sllh xan siyo magani" daga haka ya tashi ya shiga bathroom, tana nn ynda ya bar ta har ya fito yace mata ya tafi masallaci, kai ta gyada masa ya fita, sai kusan karfe bakwai ya shigo rike da leda hannunsa yana ajiyewa ya kwanta hade da rufe ido, karasawa tayi kusa da ledan ta bude taga abinci ne sai drugs, ta bude abincin ta dawo kusa da shi tace "Toh ka tashi ka ci abincin sae ka sha maganin" ba tare da ya bude idonsa ba yace "Later" da ganinsa kasan karfin hali kawai yake, ta fashe da kuka sosai, ae bae san lkcn da ya bude ido ya mike xaune da sauri ba ya kamo hannunta yace "Kuka kuma baby" ganin kukan sae karuwa yake ya mike tsaye da kyar yace "Toh xan ci yanxu" haka ta sa shi gaba yana tura abincin da kyar ko rabi bai ci ba yace "Am full dear" ita ta bude magungunan ta mika masa ya sha snn ya koma xai kwanta ta rikosa, ya kalleta a hankali yace "Baby..." Bata bari sun hada ido ba ta shiga unbuttoning din masa shirt din jikinsa ta cire gaba daya ya rage masa singlet, tace "Baxa ka yi wanka ba" girgixa mata kai yyi yace "Ltr" daga haka ta rabu da shi ya kwanta, tana xaune har aka kira isha ganin kmr bacci yake ta mike ta cire kayan jikinta ta nufi ledan kayanta me dauke da turarruka me yawa har da kaya da Zainab ta bata xata dau xani, juyowa yyi jin motsin leda, ta xaro ido ta durkushe wajen da sauri, murmushi yyi ya dauke kansa, ta dau xanin ta daura da sauri snn ta saka hijab, karasawa tayi kusa da shi ta xauna ba tare da ta bari sun hada ido ba ta taba forehead dinsa taji xafin ba mai yawa bane, bakinta kadai ne yyi motsi wajen cewa "Sorryy...." Ya jawota jikinsa ya rungumeta hade da lumshe ido, kasa yin komai tayi, tayi lamo tana jin bugun xuciyarsa, a hankali ya kai bakinsa kunnenta cikin sanyin murya yace "I love you Samantha" bata iya tace komai ba, jin hannunsa cikin hijab dinta ta kwace kanta da sauri ta mike, murmushi yyi bai bude idonsa dake lumshe ba, tayi shigewarta bayi, ko da ta fito kasa tantance ko bacci yake ko kuma idonsa biyu tayi, ta je daya side din ta durkusa tana yi tana lekensa har ta gama shirinta cikin doguwar riga mara nauyi ta feshe jikinta da turare, drink kawai ta sha don bata jin yunwa, ta xauna har kusan sha daya, ynxu kam ta gane bacci yake, jin ta fara jin bacci ta mike tana tunanin inda xata kwanta don dakin ya dau sanyi sbda ac dake kunne hakan yasa baxata iya kwanciyar k'asa ba, a hankali ta isa kan gadon ta kwanta can nesa da shi ta rakube gu daya, sai kuma ta nemi baccin ta rasa, ta gaji da juye juyenta ta mirgina a hankali kusa da shi ta taba jikinsa taji har lkcn da sauran xaxxabi, gani kawai tayi ya juyo ya jawota jikinsa, kkrin sauka ta shiga yi da sauri taji ya kirata murya can kasa, still tayi bata kuma motsi ba, ya kwantar da kansa jikinta yace "I will love you till my last breathe wife" shiru tayi bata ce komai ba, ya maidota jikinsa ta lumshe ido, a hankali yace "Can i kiss you?" bai jira amsarta ba taji bakinsa cikin nata, kasa hanasa tayi sai dai yana jin ynda xuciyarta ke bugawa, ya lumshe ido ya shiga kissing dinta daga nn kuma ya fara xarcewa ba tare da ya sani ba, hawayenta da yaji a hannunsa yasa ya kyaleta da sauri yace "Baki so koh baby?" Kai ta gyada masa, ya rungumeta sosai yace "Toh na bari..." A haka bacci ya dauketa jikinsa, bai kuma yin bacci ba, can dai ya kwantar da ita a hankali ya mike ya shiga bathroom, wanka yyi ya dauro alwala ya fito, yana xaune kan darduma kusan karfe biyu yaga tana juye juye sai kuma ta sauko daga kan gadon, mikewa yayi ya isa gabanta ya durkusa yace "What happened" daura kanta tayi kan gadon tace "Cikina" ya dagota suka xauna gefen gadon yace "Maganin ki ya kare ne?" Girgixa masa kai tayi kmr xata yi kuka tace "Na mance su can gidan" shiru yyi yana kallonta snn ya kalli agogo, sae kuma ya mike ya shiga bathroom. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By Khaleesat Haiydar📚✍🏻 _This page goes to you my Sharifath a sis frm another mum, sai ki shirya mai da ni_ 😍 61..... Ba a dau lkci ba ya fito ya dau goran swan water ya koma bayin, k'asa ya sameta xata fara kuka ya iso gabanta rike da goran da ya xuba ruwa me d'an xafi a ciki ya ajiye, ya dagota ya kwantar kan gadon, daga rigar jikinta taga xae yi ta xaro ido hade da mikewa ta rike rigar tace "Doctor..." Yace "Yea, am a doctor, ko kin mance ne" tashi take son yi kan gadon ya mayar da ita ya kwantar yace "You stay still ko in yi kwanciyata in kyale ki da ciwon ki" tace "Ehh kayi kwanciyar ka, bana so" bai kuma sauraranta ba ya kwantar da ita ya dage rigar ta rike da karfi ta sakar masa kuka tace "Ni ka kyaleni me xaka min, nace bana so" dariya ta basa ya dake yace "Xan tsayar da ciwon ne baby, ko nayi laifi? Am just tryn to be of help" kmr xata yi kuka tace "Toh dole sai ka daga min riga?" Yace "Ehh mana dear" ganin da gaske yake tace "Toh ni dai ka kashe wutan bana so" murmushi yyi yace "Wai kunyata kike ji yarinya, xa ma ki daina ne soon" daga haka ya mike ya kashe wutan dakin ya dawo, tana yi tana rike hannunsa har ya daga rigar ya dau ruwan goran, kwacewa tayi tace "Xan yi da kai na, i can my self" kallonta ya tsaya yi xata mike ya mayar da ita ya kwantar ta fashe da kuka tace "Ni nace bana so doctor, let me" kyaleta yyi, yayi kwanciyarsa ya juya mata baya, bai san ynda ta kare ba dai daga karshe yaji ta kwanta, yana jinta tana ta juye juyenta bai ko juyo ba bare yace mata komai, bayan kusan awa daya yaji tana kuka a hankali, murmushi yyi can ya juyo yana kallonta, baya ta juya masa ita ma, a hankali ya isa kusa da ita ya jawo ta jikinsa ya kai hannunsa Abdomen dinta murya can kasa yace "Kina min gardama in maki abinda xa ki ji kunya ynxu" ita dai tasan ba dainawa ciwon yyi ba amma taji ta d'an samu relief, lamo tayi jikinsa idonta lumshe, jin ya fara canxa salo ta buge hannunsa xata mike ya juyo da ita ya kankameta murya can kasa yace "Are you daring me?" bata fuska tayi ta boye kanta a kirjinsa, har kusan karfe biyu suna nn a haka yaji alamar bacci ya dauketa. Sai kusan karfe bakwai da rabi Samha ta tashi ta ga baya dakin, mikewa tayi ta nufi gun da kayanta yake ta dau brush da toothpaste ta shiga bathroom, bata yi mamakin ganin har yyi wankansa ba, tana gamawa ta fito daure da xani, ta isa gun kayanta ta dau wanda xata sa, tana durkushe gun har lkcn ya shigo dakin, kallo daya tayi masa ta dauke kai, ba karamin kyau yyi cikin kananun kayan jikinsa ba, tayi karfin halin mikewa rike da kayan a hannu ta yi hanyar bathroom, da ido ya bita kafin yayi maxa ya rikota, ta hade rai tace "Doctor bana son haka kaya xan je in...." Yace "Ba gaisuwa?" Turo baki tayi tace "Ban sa kaya ba ae" K'ara ta sakar masa a rikice ta rike xaninta ganin kwancewa xai yi tace "Bana son haka doctor, i don't like it..." Sae kuma ta fashe da kuka, ya rungumota hade da lumshe ido murya can kasa yace "Good morning wife...." Daga haka ya kai bakinsa nata, tun tana turasa tana son kwace kanta har dai ta hakura, kamar me rada ta ji yana ce mata "Are you still on ur period?" Bata iya ta basa amsa ba, yayi tambayar ya kai sau uku amma shiru, saitin kunnenta taji yana cewa "Talk plss dear" sai a snn ta bude ido da kyar, ae lkci daya wani karfi ya xo mata ta turasa a rikice ta fara ja baya tace "Doctor" fixgota yayi ta fashe da kuka sosai tace "Plss ni ka bar ni" saketa yyi ya mike daga gadon ya fice daga dakin, ko ina na jikinta rawa ya dinga yi ta mike ta dau kayanta ta shiga bathroom. Ta kusa minti talatin da fitowa kafin ya dawo dakin, ya ajiye ledan hannunsa ya kalli inda take yace "Breakfast" fingers dinta take fidgeting bata ce masa komai ba, yace "You hurry up kafin in dawo" daga haka ya fita, ta bi sa da ido kafin ta murguda baki ta mike ta bude ledan, irish ne da kwai da plantain, bata wani ci sosai ba sbda tea take son sha, kwanciyarta tayi kan gado har ta fara bacci ya shigo dakin, ya karasa ya xauna gefen gadon yana kallonta. Hannu ya kai fuskarta ta bude ido da sauri ta mike xaune, wara mata ido yayi yace "Ki shirya yanxu xa mu je gun Anty" ba musu ta mike ta nufi gun da hijab dinta yake ta dauka, yace "Baxa ki yi kwalliya ba" ta d'an kallesa kafin ta dauke kai tace "Meye shi?" Hijab dinta ta shiga sa wa ya mike ya isa bayanta tana juyowowa ta ja baya da sauri yace "Nuna maki xan yi meye shi" murmushi tayi ya jawota jikinsa yace "Hakan ma kin yi kyau sosai baby kar a kallan min ke" Yana rike da hannunta suka fita. Kawar Anty Maryam ce ta masu kwatancen gidan a waya suna isa ya ba mai adai daitan kudinsa snn ya kira yace ga su a waje, Anty Maryam ce ta fito shigo da su gidan, Abuturrab ya gaida ta kansa a kasa ta amsa tana tambayarsu ya suke, har parlon gidan suka shiga bayan ya gaisa da Hajiya Salamatu da kawarta yace xai je ya dawo anjima, daga haka yayi masu sallama ya d'an saci kallon Samha kafin ya fita parlon, barin parlon kawar Hajiya Salamatu ma tayi Anty Maryam ta kalli Samha tace "A ina ku ke yanxu?" Kanta a kasa tace "Hotel" Hajiya Salamatu tace "Ina yace maki xa ku daga nan?" Girgixa kai tayi tace "Ni ma ban sani ba" Duk suka yi shiru, can da Hajiya Salamatu tace "Ya ma sunan ki?" Samha bata dago ba sai wasa take da yatsunta a hankali tace "Samha ake ce min yanxu" Anty Maryam ta bude ido tace "Samha? Wa ke ce maki hakan?" Tace "Shi yake cewa haka duk inda muka je" Hajiya Salamatu tayi murmurshi tace "Yanxu Samha ba ki sha'awar Musulunci" Samha bata ce komai ba bata kuma dago ba, Anty Maryam ta girgixa mata kai alamar ta bar xancen, mikewa Anty Maryam tayi ta dawo kusa da ita tace "You tell me the truth Samha, abu ya taba shiga tsakaninku da shi" k'in dagowa tayi har lkcn kuma bata ce komai ba, Anty Maryam ta dago kanta tace "Nasan ba kya karya daughter kar ki fara yanxu" A hankali ta girgixa kai, Anty Maryam tace "I didn't ask you to shake ur head ki bude baki ki min magana" Da kyar tace "Bbu komai Anty" Hajiya Salamatu ta dawo kusa da su tace "Kar fa ki ji komai Samha, kar ki boye mana komai" ta kalleta tace "Allah ni bbu abinda ya shiga tsakaninmu" Anty Maryam tace "Na yarda daughter, nasan kuma irin tarbiyar da mum nd Dad suka baki" Hajiya Salamatu ta cire hijab din jikinta tana kallon gashinta tace "Kitso xa ayi mata ko retouching?" Anty Maryam tace "Tayi retouching kawai koh" mikewa Hajiya Salamatu tayi tana kallon Samha tace "Toh tashi mu je Samha akwae saloon nn anguwar ai" daga haka ta shiga ciki gun kawarta don cewa xa su saloon, tana dawowo tace "Sai ki hada abinda ya kamata kafin mu dawo Maryam" daga haka ta kama hannun samha suka fita, cikin awa daya aka gama gyaran gashin aka rangada mata lalle mai kyau ba mai yawa ba snn suka dawo gida, Anty Maryam sai murmushi take ganin ynda 'yar tata ta fito, Hajiya Salamatu na kallon Samha tace "Yaushe watan ki ke tsayawa?" Samha ta girgixa kai tace "Gobe xan gama" abubuwan da ya dace Hajiya Salamatu duk tayi mata a spare room dake gidan, ita dai Anty Maryam sa su gaba tayi. Sai kusan bayan la'asar Anty Maryam ta kira Abuturrab bayan sun mata nasiha sosai, godiya sosai Abuturrab ya dinga yi masu, ita kam Samha bnda kuka bbu abinda take, Antyn ta taji tausayinta sosai, da kyar ta yrda ta tashi Anty Maryam na rike da ita suka fita daga parlon, har bakin titi ta rakasu, sai da suka samu adai daita snn ta juya ta koma duk jikinta a sanyaye, rufe fuskarta tayi da abayar jikinta sae kuka take, ya rasa ta inda xai fara lallashinta, har ransa ya dinga jin tausayinta ya ji kmr ya rungume abarsa, kafin su isa hotel din har hijab dinta ya jike da kuka, ai suna shiga gate ya rungumeta bai damu da kallo da ya dawo kansu ba ya ja ta xuwa karkashin bishiya ya xaunar da ita kan kujera ya durkusa kan kneels dinsa gabanta da damuwa yace "Kar ki fasa min xuciya wifee, are u regretting marrying me?" a hankali take girgixa masa kai har lkcn fuskarta boye a hijab, ya lumshe ido ya bude cikin sanyin murya yace "I love you Samha, ina son ki, son da ni kai na ban san irin sa ba, i knw i will love you till my very last breathe wife, we re going to start a new life full of happiness, love nd affection, i will be ur everything, i will never disappoint you Pearl.... bbu wata bayan ke Jewel.... Look at me wife ko xan ji ddi plss i beg you" a hankali ta xame hannuwanta tana kallonsa da idanuwanta da ya kada, murmushin jin ddi yyi ya kamo hannunta, ita ma tayi murmushin a hankali, mikewa yayi ya dagota ya rungumeta gam, boye fuskarta tayi a jikinsa ganin irin kallon da ake masu a haraban hotel din. *Haske writers asso* Alhmdllh am feeling much much better now, a big tnx to my fcbk fanz for their prayers and everyone Allah ya sa mu dace, My Course mates Nafi, Sophie, Hussy.... tnx for the Jinya Allah bar mu tare mu yi ta fada, My fellow Biochemist mates tnx all for the prayers too sai mun hadu a Dept, My Nafeesat Dut. ina yin ki kawata da bata bacci idan ban yi ba, Jiddo is now Alhmdllh Allah bar xumunci. My FUD fans... Khaleesat is saying Hi.... Lng live fudites, lng live we Biochemist😅 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 62.... Washegari tun da sassafe Abuturrab ya gama shirinsa ya shiga shirya masu kayansu don kafin karfe tara yake son su bar Zaria, har ya fita ya siyo masu breakfast ya dawo bacci take bai kuma tashe ta ba, barin dakin yyi ya fita haraban hotel din yyi xaman sa, kiran Anty Maryam ne ya shigo wayarsa ya daga ya kai kunne hade da gaisheta, ta amsa tace "Dama wllh jiya na mance bn ba daughter sako ba, idan ba damuwa ka taho ka karbar mata don Allah" yace "Toh Anty xan xo ynxu" mikewa yyi ya koma ciki, wnn karan tada ta yyi, ta mike xaune yace "Am coming back soon dear ga breakfast na ajiye maki" tace "Ina xa ka?" Yace "Anty xata bada sako a kawo maki wai" kai ta gyada masa ya mike yace "You can still go back to sleep" mikewa tayi ita ma tace "Allah kiyaye hanya," daga haka ta shiga bathroom, murmushi yayi ya dau kudi da xai dauka ya fita. Takwas da rabi ya isa maraba, har parlor Anty Maryam ta shigar da shi suka gaisa snn ta dauko kudi ta mika masa tace "Dubu hamsin ne nn, ka bata bride price dinta ta siya duk abinda take so" Kansa a kasa ya karbi kudin yace "In shaa Allah Anty" Kunu da kosai ta kawo masa, bai mata musu ba ya ci, da xai tafi ya ba yaranta dubu biyu ya kuma yi mata godiya snn ya bar gidan, yayi niyyar karasawa kd gun Sadeeq amma ya kira number sa bai shiga ba hakan yasa ya koma Zaria, Samha na kwance idonta lumshe duk da ba bacci take ba, ya karasa ya durkusa gabanta yana kallonta, a hankali ta bude ido, murmushi ya sakar mata yace "Love" mikewa xaune tayi ya kamo hannunta yace "Kin yi break din kuwa?" Kai ta gyada masa ya fiddo kudin aljihunsa ya sa mata a hannu, tace "Na mene?" Ya wara mata ido yace "Ur pride price, Anty tace in kawo maki ki siya duk abinda kike so" shiru tayi tana kallon kudin, can ta girgixa kai tace "Na baka" hade rai yayi yace "Kin ban kuma? It's urs baby, me kike son in siya maki" ta kallesa tace "Ni ba abinda nake so ai, kawai kayi amfani da shi" Shafa gashin kanta yayi yace "No dear, i will get you something with it" bata kuma cewa komai ba, yyi mata light kiss ya mike yana murmushi yace "Do you still want us to go to gombe?" Kallonsa tayi bata ce komai ba, ya kuma xaunawa ya kamo hannunta yace "Kinyi shiru Pearl" tace "Duk yanda ka ce" ya dagota suka mike yace "To nace mu je can, it's more safe there" karfe sha daya saura suka bar Zaria suka dau hanyar gombe. Sai kusan La'asar suka shigo gombe, sai a snn Abuturrab ya fara tunanin da idon da xai kalli Mami, gashi ranan lahadi ce yasan tana ma gida, har suka isa gida tunani kawai yake, mai adai daitan na tsayawa kofar gidan ya kalli Samha, a hankali tace "Toh me xaka ce ma Ummi?" Fitowa yyi ya ba mai adai daitan kudinsa ita ma ta fito, murmushi yyi yana shafa kai yace "I don't know wht to say, ko xaki fadi min abinda xan ce" ta tabe baki tace "Ni ba ruwana" yar dariya yyi ya kama hannunta suka shiga compound din bayan ya amsa gaisuwar mai gadi, kamar ynda yyi tunanin hakan ne don Ummi na xaune balcony tana aiki, Samha ta xame hannunta daga nasa, a hankali yake tafiya har ya isa Balcony din, Ummi kam tun da tayi masa kallo daya dama ta ci gaba da abinda take, durkusawa yyi nan gabanta sai kuma ya rasa abun cewa, kallon Samha dake tsaye gefe tana wasa da yatsunta tayi ta girgixa kai ta mayar da dubanta kan laptop dinta, da kyar Abuturrab yyi gathering courage yace "Mami ina yini?" Kallonsa tayi kafin tace "Lafiya lau" Samha ta d'an risina ta gaisheta ita ma ta amsa snn ta ci gaba da abinda take, ganin ba magana Ummi xata yi ba ya mike, har xai bar gun tace ya dawo, dawowa yayi ta kalli Samha tace "Ki shiga bedroom dina akwai makulli a kan study table ki dauka" shiga parlon Samha tayi, Ummi na kallonsa tace "Sai da kaje ka lalata masu rayuwar ya snn ka dawo knn, i never knew takura ka nake Aliyu amma it's a promise am making now baxan sake shiga rayuwar ku ba" da sauri yace "Wllh ba haka bane Mami, gun kanwar Abbanta na kai ta kaduna, she's a muslim nd.... Mami basu bari muka bar garin ba sai da suka tabbatar na aureta, am saying nothing but d truth, kuma sai da naje kano gun Mum dina, I begged her for forgiveness, i knw i failed u Mami amma don Allah kiyi hakuri kar ki hukunta ni...." Ummi dake ta kallonsa tace "Did i deserve u going without telling me Aliyu, xan hanaka don kace min xa ku gun aunt dinta? Ni baxan hana ka ba sai dai ko in hada ku da wani ku je tare, haka kke abun ka bbu reasoning Ali?" Sunkuyar da kansa yyi kasa yace "Am so sorry Mami nasan ban kyauta ba ki yafe min" Samha na fitowa daga parlor rike da makullin Ummi tace mata taje ta bude kofa a can, tana barin gun ta girgixa kai tace "Idan ma kun tafi without knowledge dina baka da wayar da xaka kira ni daga baya?" Shiru yyi bai ce komai ba, can ta girgixa kai tace "Gaskiya i was so surprise at you, you failed my trust for you" a hankali yace "Kiyi hakuri Mami..." Tace "Anyway, tashi kaje, Allah rufa asiri, it's good she's now ur wife" bai iya ya mike ba, can ya ciro kudin aljihunsa ya mika mata yace "Aunt dinta tace in bata sadakinta, ko xa ki siya mata abu Mami" ba musu Ummi ta karbi kudin ta ajiye a gefenta, ya mike da kyar ya bar gun. Har Samha ta fara gyaran gidan kafin ya taho, yayi dusting kujera ya xauna yace "You need rest dear, drop that broom now" ba tare da ta kallesa ba tace "I can't endure resting in dirt..." Kallonta yyi sai kuma yayi murmushi yace "Toh baturiya, transform the house as you wish" kallonsa tayi ita ma tace "You watch nd see..." Kwankwasa kofa aka yi ya mike ya isa kofar ya bude, mai aikin Ummi ce tsaye ta gaishesa ya amsa snn tace "Madam tace in xo in taya ta gyaran gida" hanya ya bata yace "Alryt" bedroom ya wuce ya bar su parlon, yana sllh ya cire bedsheet yyi kwanciyarsa, kafin karfe biyar da rabi suka gyara ko ina na gidan ya rage dakin da yake ciki kawai, Samha tace "Nagode sosai xa ki iya wucewa Anty" daga haka mai aikin ta wuce ita ma ta shiga bedroom din da Abuturrab yake, karasawa tayi kansa ta ja pillon da yake kwance kai tace "You call ur self a doctor amma kuma xaka iya bacci peacefully cikin dusty room din nn?" Har lkcn bai bude ido ba, ta hade rai ta buga gadon tace "Ni ka tashi in gama gyara na, you can go to the other room and continue" bude ido yyi ya fixgota jikinsa yana kallonta yace "Ashe kin iya magana haka Samha?" Kwace kanta ta shiga yi yaki sake ta ya mike xaune yana murmushi yace "One thing about you is that, you can pretend for africa" kwace kanta tayi ta mike ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fice daga dakin snn ya mike ya bi bayanta. Da magrib mai aikin ce ta kawo masu abinci duk da ya riga ya siyo masu, yana xaune shi daya parlor yana danna laptop khadija tayi sallama ta shigo, durkusawa tayi nesa da shi tace "Uncle ashe kun dawo, ya hanya?" Yana murmushi yace "Lafiya lau khadija, ya karatu?" Tace "Alhmdllh, ina sis Samha fa?" Mikewa yayi yace "Let me check her tana ciki" daga haka ya nufi bedroom, yana shiga tana fitowa daga wanka daure da towel, tayi masa kallo daya ta wuce can karshen gado ta xauna, ya bi ta da ido, satan kallonsa tayi ganin kallonta yake ta bata fuska tace "I want to dress up..." Rufe kofar dakin yayi yace "You re free" mikewa tayi xata koma bayin ya rikota, ta wani hade rai tace "Bna so, bana son haka doctor...." Shi ma ya hade giran sama da ta kasa yace "Baki son me?" Fashewa tayi da kuka, ya buda ido yace "Ehenn, me nayi maki" ganin da gaske take ya xauna gefen gado ya xaunar da ita gefensa yace "Khadija fa na jin ki a parlor, daga magana sai ki fara min kuka?" Kallon kofar dakin tayi tana share idonta, lumshe ido yyi ya rungumeta yana shafa gashinta ya kai bakinsa kunnenta yace "Hope anjima dai baxa ki ce min baki so ba don ko kukan jini xa ki yi ba wannan xancen yau..." Shiru tayi bata ce komai ba, ya saketa yana murmushi yace "Ki shirya tana jiran ki a parlor" ta gefen ido ta hararesa ta mike ta nufi press din kayanta, ya gyada kai yana murmushi har lkcn ya fita. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 63..... Tana gama shirinta ta fita parlorn, xaune ta tadda khadija har lkcn, ta karasa tana murmushi tace "Maimakon ki shigo ciki" khadija dake kallonta ita ma tana murmushin tace "Yanxu Ummi ke ce min kun dawo sister, ya hanya" Samha ta xauna gefenta tace "Alhmdllh, ya makaranta?" Khadija tace "Lafiya lau" fruits dake cikin wani bowl Samha ta mike ta kawo ta ajiye mata tace "Rabi'ah fa?" Khadija tace "Ae har yanxu bata dawo gida ba" Samha tace "Ayya, sis fatima fah?" Khadija tace "Tana cikin gida" Apple kawai khadija ta dauka ta mike tace "Bari in je dare yyi sis Samha sai gobe" Samha ta kalli agogo tace "Da wuri haka" dariya kawai khadija tayi tace "Xan goge hijabs dina kafin in kwanta ne" daga haka ta kalli Abuturrab dake ta danna laptop tace "Uncle sai da safe" ya kalleta yace "So early Dija" murmushi tayi ta nufi kofa yace "Toh ki gayar da Mami, Yusuf na nan ne?" Ta girgixa kai tace "Yana Egypt" yace "Alryt" har balcony Samha ta rakata suka yi sallama sannan ta dawo parlor ta dau bowl din sauran fruits din ta ajiye a fridge, yace "Ke baxa ki sha ba?" Girgixa kai tayi tace "Na koshi" daga haka ta wuce daki, hijab din jikinta ta cire tayi kwanciyarta ta rufa da blanket. Sai kusan karfe sha daya Abuturrab ya gama abinda yake ya mike ya rufe gidan snn ya kashe wutan parlon ya dau laptop dinsa ya wuce daki, ajiye laptop din yyi gaban mirror ya kunna ac din dakin ya shiga bathroom don yin wanka, yana shiga bayin ta mike don dama ba bacci take ba ta dau hijab dinta ta fice daga dakin ta koma daya dakin ta shiga ta rufe tayi kwanciyarta, ko da ya fito murmushi yayi da bai ganta a dakin ba, ya gama shirinsa har da ya kwanta sai kuma ya mike ya nufi dakin da ta shiga, ta wani rufe ido kmr me bacci ya karasa kan gadon yace "Why did you leave the room" bata bude idon ba bare ta basa amsa, ya kafa mata ido yana kallo, hannu ya daura forehead dinta yace "I kiss you now idan baki bude ido ba" bude idon tayi ta mike xaune ta hade rai tace "Doctor ni fa ina ce maka bna son irin haka," kallonta ya tsaya yi can ya fixgo shoulders dinta yana mata wani kallo yace "Baki son me knn?" Ja baya tayi ta kauda kai ta tsuke baki, yace "But me yasa lkcn da kike xuwa wajena can gida bakya cewa baki son ina taba ki, you like it then koh?" Ta kallesa da sauri sai dai bata ce komai ba, ya daga kafada yace "Yeah, ynxu ne baki so but you like it then i notice" Sauka ta shiga kkrin yi daga kan gadon ya fixgota ta fashe da kuka, ji yyi ransa ya baci ya fixge hijab din jikinta yace "Sai kiyi na jini ma in ga ai" ta hade kanta da gado tana rerawa, har ya mike xai fita sai kuma ya fasa, ya dake ya xauna ya dagota yace "What's the meaning of this Samha, Where is d love?" Bata bari sun hado ido ba, ya dago kanta yace "look at me Samha" a hankali ta dago manyan idonta tana kallonsa, murya can kasa yace "Wahala kike son bani don kin ga ina son ki da yawa ko, me yasa tun da baki min haka ba sai yanxu?" Sauke idonta tayi kasa ya jawota jikinsa yace "Baki sona yanxu koh?" Kamar xata yi kuka tace "A'a" yace "Toh me yasa kike cewa baki son in taba ki" ta fashe da kuka a hankali tace "Ni tsoro nake ji" ya buda ido yace "Tsoro kuma? Tsoron me?" Bata ce komai ba kuma bata daina kukan ba, yace "Talk to me mana Wife, tsoron me?" cikin muryar kuka tace "Kai..." sosai ta basa dariya ya dake yace "Ni kuma, toh me nayi maki kike tsorona" k'in cewa komai tayi yana shafa gashin kanta yace "Ki gaya min mana tsoron me nake baki dear, baki son gani na ne kuma?" Girgixa kai tayi, yace "Then me nake maki da baki so?" A hankali tace "Bana son kana taba ni..." Shiru yyi, sai kuma yace "Why?" Tace "Saboda ni dai bana so" murmushi yayi yace "Amma da a can gida baki ce min baki so ba ai" Kallonsa tayi tace "A'a ka dai manta, duk san da ka taba ni ae bana sake xuwa sai an dade" yace "Hmmm, shknn na daina taba ki tunda baki so" daga haka ya saketa ya koma baya yace "Is that all?" Kai ta gyada masa ya mike yace "Quite alryt...." Sannan ya nufi kofa yana murmushi can underneath his breathe yace "Nasan maganin ki" bin sa ta yi da ido har ya fita kafin tayi kwanciyarta. Washegari da ya kasance monday ko kafin Abuturrab ya fito duk ta gama gyaran gidan gaba daya tayi wanka ta shirya cikin abayarta, Tun takwas mai aiki ta kawo masu breakfast in ji Ummi, Kallo daya yyi mata yayi xamansa parlor yana kkrin bude laptop dinsa, tace "Ina kwana?" Ba tare da ya kalleta ba yace "Lfya baby" tace "In kawo maka breakfast din yanxu?" Ya girgixa kai yace "Nop" kwankwasa kofa aka yi ta mike ta isa kofar ta bude, Fatima ce tsaye sanye cikin abaya da jaka a hannunta ta sa siririn glass a ido Kallon kallo suka dinga yi na kusan second goma, can Samha ta dake tace "Ina kwana" Fatima tace "Alhmdllh, Doctor na ciki?" Kai kawai Samha ta gyada mata, d'aga wayarta dake ring tayi ta bi ta gefenta ta shige parlor Samha ta bi ta da ido, Tsaye tayi d'an nesa da shi tana ci gaba da waya da kawarta da ta kirata, Abuturrab da bai dago ba tun shigowarta, cab ya juya ya kalli bakin kofa suka hada ido da Samha kallon Fatima da ke kkrin mayar da wayar jaka bayan ta gama yyi, ta dago suka hada ido, kirkiran murmushi yyi yace "Morning" sosai tayi mamakin hakan ita ma ta mayar masa da na yake tace "Good morning" yace "Ya boko?" Tace "Alhmdllh" idonsa ya mayar kan laptop yace "Wani course kike?" Tace "MBBS" kallonta yyi daga kasa har sama kafin yace "Lvl?" Tace "300" yayi d'an murmushi yace "Nyc" Tace "Thank you" ya mayar da dubansa laptop yace "Welcome" "Dama Ummi ce tace ka je" ta fadi hakan tare da juyawa tayi hanyar kofa yace "Alryt" Samha na nan tsaye inda take tun shigowar fatima, Abuturrab ya saci kallonta ya dauke kai ya ci gaba da abinda yake, fatima na fita ko rufe kofar Samha bata yi ba ta nufi hanyar daki, ya kalleta da sauri yace "Dear a ban break din yanxu i think am hungry" ko kallonsa bata yi ba ta shige daki, yar dariya yyi ya mike ya fita xuwa kiran Ummi, suna gaisawa tace "Are you still interested with the job or i give someone?" Yace "I am Mami" tace "When re you resuming?" Yace "Probably today" tace "You leave it tomorrow" godiya yyi mata ya mike ya bar parlon, yana komawa part dinsa tea kawai ya hada ya sha ya fita, compound ya tadda khadija ya sa ta dauko masa makullin mota ya fita siyo masu foodstuffs, sai kusan karfe goma ya dawo gidan mai gadi ya taimaka masa fiddo kayan abincin xuwa cikin gida, shi kuma ya karasa da su kitchen, bedroom din da take ya nufa ya ganta kwance idonta rufe, karasawa yyi ya xauna gefenta ya kamo hannunta yace "Baby baki ban breakfast ba fahh" mikewa tayi xaune kmr warce aka tsikara tace "But i told you, i warned u bana son kana taba ni, i don't like it...." Kallon ynda ta hade rai sosai yake yi, can ya mike yace "And that's because i forgot" daga haka ya fice daga dakin. Makullin mota ya kuma dauka ya fice daga gidan, bai dawo ba sai bayan isha ya samesu tare da khadija a parlor, khadija ta gaishesa ya amsa da fara'a ya wuce daki, ba a dau lkci ba khadija ta wuce ita ma ta mike ta shiga daki, kwanciya tayi don tayi wanka, can ta gaji ta mike xaune ta hade kai da gwiwa sai hawayen da bata san dalilinsa ba, ta kusa awa biyu a hakan, can ta mike da kyar tana kallon agogo taga karfe goma, tashi tayi kamar mara lafiya ta fita dakin ta wuce nasa, dai dai fitowarsa wanka yana sanye da bathrobe yana goge gashin kansa yyi mata kallon gefen ido ya xauna bakin gado yace "Baby baki yi bacci ba" bata ce komai ba shi ma bai kalleta ba, yana ci gaba da goge gashin ya jawo wayarsa yana danne danne, still ba tare da ya kalleta ba yace "Hope kin ci abinci?" Nan ma bata ce masa komai ba ya mike ya isa gun kayansa ya fiddo pyjamas dinsa, muryarta ya ji a hankali tace "In kawo maka abinci?" Yace "No baby, na ci abinci a waje..." Daga haka ya nufi gaban mirror ya shafa man da xai shafa a gashin kansa ya sa turare, sai a snn ya juya ya kalleta yace "Hope kema kin ci abincin?" Hawaye ya gani idonta, ya buda ido yace "Toh kuma, did i still touch you?" Juyawa tayi ta fita daga dakin, ya girgixa kai ya ci gaba da shirinsa ya gama saka sleeping wear dinsa snn ya fita dakin ya shiga nata, bai ganta a bedroom din ba sai sautin kukanta da ya dinga ji a bathroom, bathroom din ya shiga da sauri ya ganta durkushe tana rera kuka, da mamaki yace "Are you okay Samha?" Hade kanta tayi da gwiwa, ya dagota ta kuma rushewa da kuka ya ja ta suka fita bayin, xaunar da ita yyi gefen gado yace "What's d meaning of all this Samha, kina da damuwa ne?" Rungumeta yyi ganin ba shiru xata yi ba yace "Samha me yasa kike son ki dinga tada min hankali" dago kanta yyi yana kallonta taki bari su hada ido, hade bakinsa yyi da nata yana kallon idonta, ta rufe idon da sauri, ya kwantar da ita a hankali ya fara sarrafa ta, sun dau lkci me tsayi kafin ta bude ido da kyar xuwa lkcn ko ina na jikinta bari yake, dai dai kunnenta cikin sanyin murya yace "Baby don't tell me no plss, you've punished me enough" ta fashe da kuka tace "Doctor noo" daga haka ta turasa iya karfinta ta ja bargo har kanta, wani irin kallo yake mata na kusan minti biyar kafin ya mike ya fice dakin. Washegari tun bakwai ya bar gidan tana kitchen tana hada breakfast ya gama warming mota ya dau hanyar clinic, Tana jin fitansa dama ta kashe komai ta koma daki tayi kwanciyarta. *Haske writers asso* Sorry!! 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 64..... Kusan a tare suka shigo compound da fatima da yamma, bai je parkn space dinsa yyi parking ba yayi a compound din ita ma haka, Samha da khadija da mai aikinsu na xaune gaba dayansu a balcony dinsu khadijan, Abuturrab ya kulle motarsa ya d'an kalli fatima dake kkrin kulle mota, suka hada ido tace "Ina yini" yace "Lfya lau, ya lectures" tace "Ban yi lectures ba yau, had an attack da safe" yace "Subhanallah, bakya fita da mask ne" Ta girgixa kai tace "I don't" duk hankalin Samha na kansu duk da hiran da mai aiki ke masu, Abuturrab yace "May be you re enjoying d attack" murmushi tayi tace "not really" Mikewa Samha tayi tana kallon su khadija tace xata shiga gida daga haka ta bar wajen, Abuturrab ya amsa gaisuwar Khadija yana murmushi, kallon fatima yyi yace "Sai da anjima" daga haka ya bi bayan Samha ko kafin ya iso har ta rufe kofar parlon gam, ya murda ya shiga ya ga har ta kusa daki, xama yyi parlor ya cire suit din jikinsa da safa sai necktie, can ya mike ya wuce daki don yin wanka yana fitowa ya bar gidan gaba daya xuwa gidan abokinsa Dr Sharif. Sai bayan isha ya dawo gida, har xai shiga dakinsa sai kuma ya shiga nata durkushe ya ganta bakin gado idonta lumshe, bude ido yyi yana mata kallon mamaki, can ya karasa ciki yace "Meye haka kike?" Bata tanka sa ba bata kuma bude idon ba, yyi tsaye yana kallon ikon Allah har ta bude idon ta mike, yace "Me kike haka Samha?" Tace "Idan an kira sllh, me kke xuwa yi masallaci?" Daga haka ta karasa tayi kwanciyarta kan gado, kasa ce mata komai yyi, can ya tabe baki yace "Wai nn addu'a kika yi?" Bata tanka sa ba ya karasa gadon yace "I see! Sae bayan watanni da yawa ku ke addu'an naku knn? Ke a Christians dinma rakiya kika yi" kallonsa tayi da sauri, can tace "Haka kace min?" Yace "Yes, wani gulma ne xaki wani durkusa bakin gado ki hade hannaye abinda ba yi kike ba" hawaye ne ya cika idonta ta dauke kanta ya juya ya fita, kasa bacci Abuturrab yyi daren ranan, ya mike xaune ya dafe kansa, can ya mike ya fita, yana bude kofar dakinta ta juyo suna hada ido ta dauke kai, tsaye yyi bakin gadon yana kallonta, can ya xauna yace "Samha" bata juyo ba bare yasa ran amsa, ya shafa kansa a hankali yace "I am sorry, i don't mean those words, donno knw what came over me, kiyi hakuri don Allah" har lkcn bata yrda ta juyo ba, ya dagota ta kwace kanta ta ja baya tana kallonsa shima kallon nata yake, ta kauda kai tace "ni ban ji haushi ba, to don me ma xan ji haushi bayan ni na siyar ma kaina, i know as far as i disobeyed my parent, neglect dem just like that for my selfish reasons xaka iya fada min abinda ya fi haka at anytime, God knws best, shi yasan dalilin da yasa na yrda na xabe ka a kan iyayena just within watanni biyu xuwa uku da haduwar mu, ni tawa kaddarar knn...." Tana magana ne hawaye na sakko mata, Saurarenta kawai yake har ta kai karshe kafin yace "Kmr ynda kika xabe ni kan iyayen ki nima haka na xabe ki kan iyayena you have no reason to be uttering this, kin san soyayyar dake tsakanina da mahaifiyata har na yrda taki ke neman rinjayar tata, i said good bye to peace, luxurious life nd rest of mind frm d very first day i saw you Samantha...." Tsam ta mike tace "Same with me, nd i pray this to end soon, m tired nd bored of this miserable life" daga haka ta fice daga dakin ya bi ta da ido, ya fi minti biyar xaune inda ta bar sa, can ya gyada kai ya mike ya fita ya koma dakinsa. Washegari kmr jiya tana kitchen ya fice daga gidan ya wuce parking lot, tana jin ya ja mota ya bar compound din, ta gama juye ruwan Lipton da ta daura ta bar kitchen din ta shiga dakinta ta fara gyarawa daga haka tayi kwanciyarta, sai kusan sha biyu ta tashi, ta shiga bathroom tayi wanka, cikin riga da skirt na atamfa ta shirya ta fito parlor, nan ta fara tsaftace parlon ta goge ko ina snn ta shiga bedroom dinsa nn ma ta gyara ko ina ta wanke bathroom ta fito, tea ta hada da soyayyan kwai ta ci ta kwanta parlor tana nn kwance har uku, duk ta gaji da tunane tunane don bata san wani iri xata yi ba kuma taji an bude gate, mikewa tayi ta isa window kusa da kofa tana leken wanda ya dawo, parking yyi ya fito, tun daga nesan take kallonsa ko kiftawa bbu har ya iso Veranda ya bude kofar parlorn ya shigo, ya tsaya na kusan second goma yana kallonta, can yyi yake yace "What r u doin here" daga haka ya karasa cikin parlon ta bi sa da ido har ya shiga daki, dawowa cikin parlon tayi ta xauna kan kujera, tayi xaman kusan rabin awa a gun kafin ta mike ta shiga dakinsa tagansa kwance har ya fara bacci, durkusawa tayi kusa da shi tana kallon dogayen lashes dinsa, a hankali ta sauke idonta kan pointed nose dinsa dake kara masa kyau snn ta kalli lips dinsa, mikewa tayi jiki a sanyaye ta juya ta nufi kofa ta bude, ji tayi yace "Samha" ta juya da sauri tana kallonsa ya mike xaune yace "You want something?" Girgixa kai tayi tace "Wanted asking what to cook" yace "Noo, am full dear, ki dafa ko me kike so, m nt hungry" kallonsa take ko kiftawa bbu, sai kuma ta juya ta fita ya koma ya kwanta. Yana danna laptop bayan magrib wayarsa dake gefensa ya fara ring ya jawo yana kallon screen din ya ga Mami ce ke kiransa, dagawa yyi ya kai kunne hade da lumshe ido yace "Mum...." Daga daya bangaren tace "Aliyu, ya ku ke?" Yace "Lafiya lau Mami, ya gidan" tace "Good, bbu damuwa dai koh?" Yace "Babu Mami, ya siblings dina, i knw i so missed them mum" tace "They r all fyn, ya matar taka? Don't even knw her name" murmushi yyi don yaji ddin tambayar har ransa, yace "Sunanta Samantha Mami, amma Samha ake ce mata" Mami tace "Ohk, where is she?" Mikewa yayi yace "Bari in kai mata wayar" Tsaye ya ganta bakin window a dakin, ta juya tana kallonsa ya mika mata wayar yace "My mum" karba tayi ta kai kunne hade da sallama, daga daya bangaren Mami tace "Ameen, ya kike?" Sunkuyar da kai tayi tace "Lafiya, Mum ya gida" Mami tace "Alhmdllh, sai ayi ta hakuri kin ji, Allah maku albarka" Kai ta gyada mata kmr tana ganinta murya can kasa tace "Ameen mum nagode" Daga haka Mami tace "Ba shi wayar" mika masa tayi ya karba ya juya ya fita ya koma parlor, suna gama wayar ya mike ya fita don siyo abinci, a tare suka shigo gidan da Ummi, yyi parking ya fito ya nufi motarta, gaisheta yyi ta amsa tana kkrin fiddo system dinta da kayan dake bayan mota, karba yyi ta sake masa tace "Ya Samha?" Yace "Tana ciki" daga haka yyi part dinta ya bude kofar parlon hade da sallama ya shiga, khadija ce ta fito daga daki, ya ajiye abubuwan hannunsa yace "How you?" Tace "Fyn uncle, ya aiki" yace "Alhmdllh" ya kalli fatima dake xaune a kujeran parlon ta jinginar da kai tana bacci hannunta rike da pen, ga stool gabanta da textbooks sai handouts da fulls cap sheet, kallon khadija dake dariya yyi yace "Is she okay?" Tace "Tun daxu take bacci fah, wai kuma assignment 3 xata yi a nn" Shigowar Ummi yasa yyi murmushi kawai bai ce komai ba, Ummi na kallon fatima tace "Kee" buda ido tayi da sauri, Ummi tace "You re deceiving ur self" Tattara takardun ta shiga yi kmr xata yi kuka tace "Ummi na gaji wllh, i still haven't done the assignments, har library na shiga a sch but to no avail, am having a serious headache...." Sai a snn ta lura da Abuturrab, Ummi tace "Ni dai nace maki kina yaudaran kan ki ne, ya wuce ki dawo gida mu xauna ko kuma ayi dumping dinki Zoology ko Botany" daga haka ta yi gaba abun ta, Fatima ta kalli Khadija dake dariya tace "Leave now" juyawa tayi ta bar parlon, ta mike tana ci gaba da tattara takardun ba tare da ta kalli Abuturrab ba tace "Good evening" yace "Evening, wani assignment ne?" Sai a snn ta kallesa kamr xata yi kuka tace "Gasu nan" daukar questions din yyi yana kallo, can yace "Alryt, kiyi kkrin yin wnn it's nt complicated, i will try nd do the other two" daga haka ya juya ya fita da questions din a hannunsa ta bi sa da kallo. Yana fita mota ya nufa ya dauki abincin da ya siyo ya shiga gida ya ajiye takardan a parlor ya karasa dakin da Samha take, ajiye mata ledan yyi ganin idonta biyu yace "Na ga baki yi girki ba, ga abinci" ko rufe baki bai yi ba tace "Am full" ya kalleta snn ya dau abincin ya fita, sai da yayi isha yyi wanka snn ya ci abinci, yana gamawa ya jawo laptop ya fara duba mata assignments din, ba shi ya gama ba sai kusan sha daya da rabi, ya kashe system dinsa ya ajiye takardun a kai snn ya nufi daki, har xai shiga nasa dakin sai kuma ya juya ya bude nata, xaune ya ganta can karshen gado ta jinginar da kanta jikin gadon idonta lumshe, ya isa kusa da ita ya xauna yana kallonta, wani tausayinta da sonta ya dinga ji har cikin ransa, ya hura mata iska a fuska yace "Baby ba ki kwanta ba?" Bude ido tayi ya tsura ma idanuwan nata da yyi ja nasa idon, a hankali yace "You cried Samha, what's wrong" bata ce masa komai ba, ya lumshe ido yace "Toh ya kike son in maki Wife, kince baki son ina taba ki, am avoiding that, then what's it again" hawaye ne ya shiga sakko mata tace "Noo, u re avoiding me because i didn't give u my self, dama ba saboda Allah kake sona ba sha'awata kawai kake ba sona kke ba" tana fadin hakan ta fashe da kuka. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 65..... Ido ya xuba mata yana kallo, sai kuma yyi murmushi yace "Is that what you re thinking?" Ko kallonsa bata yi ba, ya langwabar da kai yace "Alryt idan Allah ya yrda na daina daga ynxu, xan yi ta kallon ki kmr photo kmr ynda na fara daga jiya, but bna son wnn koke koken da kike yi pls" sai a snn ta kallesa tace "Toh kuma ni bna son interaction din ka da mata" ya d'an bude ido yace "Mata kuma, wace macen kika ga ina interacting da?" Tace "Ka fi ni sani ai" murmushi yyi yace "Toh ae dole in dinga interacting da mata baby, have you forgotten am a Doctor?" Tace "Ae ba a clinic nace ba" shafa kai yyi yana murmushi yace "Toh ba gwara ko ma a ina ne in yi interacting da su ba ko Allah xae ban warce xan aura da baxata dinga hanani taba ta ba Dear, or do i look like a waliyyi to you?" Wani kallo take masa kafin ta mike ya rikota yace "Ina kuma xaki baby" bata fuska tayi ya lumshe ido ya jawota jikinsa ya rungume yace "Am sorry, i just can't Samha, baki da tausayi, i tried my best na ganin banyi disfiguring din ki ba throughout our stay together, ba kowa ne xai iya yin haka ba amma ke duk baki ga haka ba, i don't knw ko jan aji kike min, dear baki san wahalan da na sha na ganin ban bata ki ba, pls allow me show you hw i love you" lamo tayi jikinsa, ya kai bakinsa kunnenta yace "Plss" girgixa masa kai tayi tace "Some other day..." Murmushi yyi yace "Ohk den..." Daga haka ta janye jikinta tayi kwanciyarta, ya mike ya kashe wutan dakin ya dawo ya kwanta shi ma. Washegari da asuba yana dawowa masallaci ya shiga bedroom dinsa, kafin karfe shidda da rabi ya fito parlor har ya shirya, ya xauna ya bude laptop, daga kitchen ta fito ta gaishesa yana duba assignment din fatima da yyi jiya ba tare da ya kalleta ba yace "Morning wife, har kin tashi" tabe baki tayi ta koma kitchen sai a snn ya daga kai, bayan minti goma ta fito rike da flask da cup ta karaso gabansa ta durkusa ta ajiye, yace "What's that?" Ko kallonsa bata yi ba ta mike ta koma kitchen ta dauko tray mai dauke da irish da kwai sai bread ta ajiye gabansa ta dau cup ta fara hada shayin, yace "Alryt just coffee" mikewa tayi ta koma kitchen ta dauko coffee powder, danna bell din parlon aka yi ta kallesa kafin ta mike ta isa kofar ta bude, fatima ce tsaye tana sanye da hijab har kasa sai hand bag dake rataye shoulder dinta tace "Morning doctor na ciki?" Kallonta kawai Samha take, can ta juya ta koma ta durkusa ta ci gaba da abinda take, mikewa Abuturrab yyi ya dau fullscaps din ya nufi kofa, gaishesa fatima tayi yace "How you" daga haka ya mika mata yace "You rewrite it if you wish..." Kallon diagrams din da yyi mata drawing kawai take, ta kallesa tace "You draw fine" daga kafada yyi yace "Sometimes" tayi murmushi tace "Am grateful MD" yace "Say not... Kin yi dayan?" Ta gyada kai tace "Ummi ta min" yace "Good" godiya ta kuma yi masa tace "Ina da lectures 7, see yah" daga haka ta juya ta wuce ya rufe kofar, komawa yyi yana murmushi ya xauna ya karasa hada coffee dinsa, sai karfe bakwai ya mike ya rufe laptop dinsa ya wuce dakinta, kwance ya sameta ya rungume hannayensa yace "Why did you make an uncomplete coffee for me nd left?" Ko kallonsa bata yi ba, yace "Aiit, am off to work baby" daga haka ya fita, tana jin fitar mota ta fashe da kuka. Yanda ya fita haka ya dawo ya tarar da gidan da yamma, ko mamaki bai yi ba ya wuce daki yayi wanka ya canxa xuwa kananun kaya snn ya fito ya shiga dakinta, tana xaune hannunta rike da glass din hollandia drink ya xauna bakin gadon yace "Yau wife din hutu take kenan?" Bata ce komai ba yace "Toh ina yini?" Dauke kai tayi, yace "Tohhh har da axumin magana kenan" mikewa yyi yace "Aitt, let me go get something to eat am famished" daga haka ya fita daga dakin, a xuciyarsa kuwa tunanin ynda xai yi maganinta cikin ruwan sanyi yake. Take away biyu yyi masu ya ajiye mata nata a parlor ya shiga daki da nasa, sai kusan karfe biyar ya ji ta fita parlor yyi murmushi yana ci gaba da kallonsa a system, ana kiran magrib ya fita, gani yyi an gyara parlon ya tabe baki ya fita, bai dawo gidan ba sai bayan isha, kitchen ya shiga ya dauko glass cups biyu yyi xamansa a parlor, ya dau fura da nono mai sanyi da ya siyo ya xuba a cups din biyu, mikewa yyi ya shiga kitchen ya dau wani cup din ya xuba ruwa kadan a ciki, ya ciro satchet din pill a aljihunsa ya bude biyu ya xuba a ruwan ya mayar da pill din aljihu, yana tsaye har maganin ya narke ya dau spoon ya juya ya bar kitchen din, a glass cup daya ya juye ya sa cokalin ya juya ya mayar da furan gefe ya koma kitchen ya wanke spoon din ya ajiye ya dawo parlor, sai da ya shanye nasa gaba daya snn ya dau wanda ya xuba pills din a ciki yayi d'an murmushi ya nufi dakinta, tana xaune gaban mirror daure da towel alamar daga wanka ta fito tana packing gashin kanta, ajiye cup din yyi ya xauna bakin gado yace "Baby yau duk kin share ni ko, baki damu da na ci abinci ba ko ban ci ba, is that fair?" Ba tare da ta kallesa ba tace "I thought warce kake yi ma assignment at midnyt ta kawo maka ai" yace "Uhm ae ba matata ce ita ba da xata kawo min abinci" tace "Toh sai ta xama mana ta dinga kawo maka" yace "May be soon.... Nasan ita baxata dinga bari na da yunwa ba ina fita siyan take away" kallonsa tayi, ya wara mata ido ya mike ya isa gabanta mikewa tayi da sauri ya rikota yace "When i say you, i mean you baby, kullum son ki karuwa yake a raina duk da sabbin walakancin da kika tsiro ynxu wife..." Kamar xata yi kuka tace "Ko dai kai ne ke min wlknci" yace "A'a baby, ni da kike bari da yunwa, you re starving me...." Turo baki tayi tace "Kwanan nn ae ko nace me xan dafa ce min kake you are full, i thought you r always full ai" murmushi yyi ya karasa gun cup din furan da ya ajiye ya dauko ya ajiye mata gaban mirror yace "Alryt ga fura da nono, it's chill, naga ko na siyo maki abincin ma ba ci kike ba..." Daga haka ya juya ya nufi kofa yace "Let me take my bath" Yana fita ta karasa press dinta ta fiddo kayan baccin da xata sa, sai da ta gama shiryawa ta saka net a kanta ta daura xani snn ta nufi gado ta kwanta, mikewa tayi ganin furan da ya ajiye mata ta dau cup din don bai shiga ranta ba, beside ita ba ma'abociyar son fura da nono bace, bathroom ta shiga ta xubda rabi kar dai yace bata sha ba snn ta fito ta wuce parlor roban furan ta gani ajiye parlor ta karasa ta durkusa ta dauka taga da saura a ciki, ta bude ta juye snn ta shiga kitchen ta wanke cup din ta ajiye ta wuce daki ta kwanta, sai kusan karfe goma Abuturrab ya fito parlor yana sanye da pyjamas dinsa ya xauna ya bude laptop, sauran furan dake ajiye ya dauka ya bude ya fara sha, bai shanye gaba daya ba ya ajiye ya ci gaba da abinda yake, bayan kusan minti goma ya juya a hankali yana kallon furan. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 66..... Jinginar da kansa yyi jikin kujera ya lumshe idonsa na kusan minti ashirin can ya bude idon a hankali ya mike, bedroom dinsa ya nufa ya kure ac yyi rub da ciki a kan gado, tun yana controlling kansa yana daurewa har ya kasa, kawai ya tashi ya fita, dakinta ya shiga ya ganta kwance har tayi baccinta, Da kyar ya isa gadon ya fada kai, ta mike da sauri tana kallonsa don baccinta bai yi wani nisa ba, karasawa tayi kusa da shi da mamaki tace "Me ya faru doctor" jawota yyi jikinsa cikin sarkewar murya yace "Samha don't tell me noo....." Kwace kanta tayi ta fara ja baya a tsorace ganin yanda idonsa ya sauya kala, ya fixgota ta fasa ihu a rikice tace "Ni ka kyaleni" ya rufe bakinta, kokuwa ta fara yi da shi da hannu daya ya riketa ta kasa motsi, tayi mugun tsorata ganin yanayinsa cikin kuka sosai tace "Noo doctor plss kar ka yi min haka, don Allah ka daina, i can'ttt" kamar ba da shi take ba haka ya mayar da ita yanda yake son ganinta gabansa, iyakar rudewa ta rude, ta dinga kuka tana son tashi amma ta kasa duk jikinta ya mutu, a ranan ce rana ta farko da yaji ta kirasa da Aliyu, bbu kalan rokon da bata yi masa ba amma kamar tana kara tunxurasa duk da shi kansa ba a son ransa bane, sai take ganin kmr ba shi da ta sani dake kyaleta idan ta fara kuka ne gabanta ba, ta rufe ido ta dinga kiran Mumy ko ina na jikinta na bari, lkci daya ta hadiye kukan da take ta xaro ido hade da kwala ihu yyi saurin hindering dinta daga ci gaba da hakan ta hanyar rufe bakinta, wani karfi ya xo mata xata mike ya nuna mata karfinsu ba daya ba, daga wannan lkcn sama sama ta dinga sanin abinda ke faruwa daga karshe kuma bata kuma sanin komai ba sai bude ido tayi a hankali ta gansa xaune gefenta yana hada allura, ji tayi kmr jikinta ba nata ba ga wani ciwon kai da yasa ko bude idon bata iya yi sosai ko hannunta ta kasa dagawa, juyowa yyi ganin idonta bude ya dawo kusa da ita da sauri yace "Wife...." da kyar tace "Doctor kai na, i don't knw...." Kasa ci gaba tayi don ba sosai ma maganar ke fitowa ba, ya dafa kanta da yyi xafi sosai da damuwa yace "Xai daina baby, am sooo sorry, i never meant that..." kallonsa take kmr me son gane ma'anar abinda yake cewa, lkci daya incident din few hours ago ya fado mata ganin idonsa da bai dawo dai dai ba har lkcn, ta tuna abinda take ji bbu banbanci da wanda taji daxu, ja baya tayi ta fasa ihu wani karfi ya xo mata ta mike da sauri ya rikota ta fashe da kuka mai ban tausayi jiki na rawa tace "Plss kayi hakuri Aliyu, wllh mutuwa xan yi....." Ya rungumeta gam ya lumshe ido jin xafin jikinta cikin sanyin murya yace "Am sorry Samha... It's nt intentional, i...." Turasa kawai take tana kuka sosai duk a tsorace take tana cewa "Don Allah ka sake ni plss" yace "Toh ki bari in maki allura your temperature is high...." Wani k'aran da ta sakar masa bai san lkcn da ya cikata ba, ta sauka kan gadon kawai ta durkushe nn bakin gadon jin ba iya barin gun xata yi ba ta dinga rusa kuka, tunda take bata taba jin abinda take ji a lkcn ba, duk ya ji tausayinta ssae amma ya kasa xuwa inda take, can dai yyi ta maza ya mike, ba wahala kadan ta basa ba kafin yyi mata alluran relieve hade da na bacci, kuma lkci daya baccin ya dauketa ya kwantar da ita ya xauna gefenta yana da ya sanin abinda yyi at the 1st place, har aka kira asuba bai rintsa ba ya mike da kyar ya shiga yyi wanka ya dauro alwala ya fito ya fita xuwa masallaci, ya jima xaune bayan an idar yana Azkar kafin ya koma gida, bedroom dinsa ya shiga don dauko disinfectant a bathroom, yana shiga wayarsa na katsewa dauka yyi yaga kiran Ummi da Dr Sharif, Ummi ya fara kira ta daga suka gaisa yace "Ummi ina masallaci ne" tace "Alryt baku yi magana da Sharif din ba knn?" Yace "No, mis call na gani shi ma bari in kirasa" tace "Okay" daga haka ya katse ya kirasa yana dagawa suka gaisa Dr Sharif yace "Ummi ce dama tace in kira ka, in the next 1 hr xa a shiga da matar nn theatre Dr Mubarak bai nan haka Dr Amina.... I think you have to come over da wuri" Shiru Abuturrab yyi kafin yace "Sharif my wife is sick i can't leave her a halin da take yanxu...." Dr Sharif yace "Subhanallah, Allah ya sauwake mata, but ka kira Dr ka fadi mata she will come over ita" Abuturrab yace "Alryt.... Bari in kirata" daga haka ya katse ya kira Ummi tana dauka yace "Mami, Mun yi magana da shi amma Samha bata da lafiya....." Ummi tace "Subhanallah me ya sameta?" Ya shafa kai yace "Zazzabi Mami, yanxu ma pharmacy xan fita siyo mata drugs" Ummi tace "Is it that critical?" Ya d'an yi shiru kafin yace "Ehh Mami, bata samu bacci jiya ba, i think it's malaria probably with typhoid" Ummi tace "Alryt ka siyo treatment din bari in taho" buda ido yyi sosai yace "emm, noo Mami, ae Mami da ki bari kar ki yi wahala, it's too early, i think it's nt critical" shiru tayi sai kuma can tace "Just to see her condition ne dama, or is she pregnant ne kke boyewa" Ya kuma buda ido yace "Nnoo Mami, i.. I.... Just notice she's very sick jiya da daddare, just sick..." Tace "Toh gani nn xuwa" bai iya yace komai ba, ya juya da sauri ya koma dakin da take, bedsheet din ya rufe, ya d'an gyara dakin ya lullubeta ya fita ya dau makullin mota, a balcony suka ci karo da Ummin ya kuma gaisheta tace "Ina kuma xa ka?" Yace "Amm Mami tunda xaki dubata bari in je clinic din kawai, yace min Dr Mubarak ma bai nan" daga haka ya kara gaba ta bi sa da ido, can ta karasa cikin parlon ta wuce dakin da ta gani bude, kan gadon ta karasa tana kallonta ta dafa goshinta tace "Samha" kallonta kawae take jin xafin jikinta, da kyar Samha ta bude ido ganinta tace "Ummi" Ummi ta dagota tace "Ina ke maki ciwo daughter, tun yaushe ne baki da lfya?" fashewa da kuka tayi, Ummi tace "I didn't ask you to cry, ina ke maki ciwo" ta rike kanta cikin kuka tace "Ummi kai na" Dagota Ummi tayi ta saki wani kara, da mamaki Ummi tace "What happend" tana rike da hannunta tace "Ummi baxan iya ba" Ummi tace "Baxa ki iya me ba me ya sami kafar" bata ce komai ba sai kuka, Ummi tace "Toh tashi tsaye" girgixa kai ta dinga yi hawaye na sakko mata, Ummi ta dagata da kanta amma ta durkushe nn kasa da sauri, mamaki ya cika Ummi, ta dai dake tace "Kin ji ciwo a kafar ne nace?" Girgixa mata kai tayi, shiru Ummi tayi kmr me son gano abu, can ta kalli gadon, bude gun xanin gadon da ke rufe tayi tana kallo, can ta rufe ta kalli Samha a hankali tace "It's okay daughter daure ki tashi let me help you" sosai Ummi ta tausaya mata don iya daurewa ta daure, ta bata tea da magani ta hadiye snn ta sa ta ta kwanta sai bacci. Ta kimtsa ko ina na dakin ta fita, haka kawai taji Abuturrab ya burgeta ta sake yarda da shi fiye da ynda tayi a da sai dai kuma haushinsa ne cike a ranta, is he on his Right senses?? sai kusan karfe sha daya, a kofa suka kusa cin karo don ta shigo duba Samha dake ta bacci, kasa barin su hada ido yyi ya koma baya sai kame kame yake, ta juya ta koma cikin parlon ya bi bayanta. *Haske writers asso* _Am also under NLC don haka na tafi nima ehe_🙄 💫 *Noorul Huda*💫 By Khaleesat Haiydar📚✍🏻 67..... Yana ganin ta xauna yace "Mami, it was successful...." Ummi tace "Maa sha Allah" ba tare da ya bari sun hada ido ba yace "Dr Mubarack came afterward" mikewa tayi tace "Alryt it's good" daga haka ta nufi kofa ya bi ta da kallo yana son yi mata godiya amma ya kasa, sae da ta fita ya mike ya shiga daki, kwance ya ganta tana bacci, ya xauna gefenta yana kallonta, hannu ya daura forehead dinta a hankali ya ji jikinta ba xafi, wani sabon sonta yake ji har cikin ransa, yyi murmushi tuna incident din jiya, ya kasa daina mamakin ynda lamarin ya faru, is it that xuwa tayi ta juye masa furan da ya bata, ya kai fuskarsa nata ya lumshe ido murya can kasa yace "I will always love you my wife" pecking dinta yyi ya gyara mata dogon gashinta, a hankali ya yaye bargon jikinta, yar riga ce iya gwiwa jikinta ya daga rigar, motsi ta fara yi ya sauke rigar da sauri, ta juya masa baya ta ci gaba da baccinta, ya kusa minti goma yana kallonta, dubata yake son yi amma bai san ta yaya ba don bai son ta tashi, can ya mike ya shiga bathroom. yana shiryawa a dakinsa bayan ya fito wanka aka danna bell, ya karasa buttoning din shirt dinsa snn ya fita parlor, Mai aikin Ummi ce tsaye da breakfast a hannunta ta gaishesa ya bata hanya ya amsa gaisuwarta ta shiga ta ajiye break din snn ta fita, ya xauna parlon yyi danne dannensa a laptop snn ya hada shayi, yana gama shan shayin ya jinginar da kansa jikin kujera ya lumshe ido moment dinsu jiya ya dinga dawo masa, murmushi yayi underneath his breathe yace "She's kinda different" kiran sllhn Zuhur ya sa shi bude ido a hankali, bayan minti biyar ya mike ya nufi dakinta, xaune ya ganta a kasa ta jinginar da kanta jikin gado, ta daga ka suna hada ido tayi saurin kawar da kanta, ya karasa gabanta a sanyaye ganin hawaye idonta ya durkusa gabanta yana kallonta, bata bari sun hada ido ba amma da ganinta kasan a tsorace take, sae wasa da yatsunta har lkcn hawaye na sakko mata, sae duk ya ji tausayinta deep down him, cikin sanyin murya yace "Am.... am sorry Samha... Forgive me plss." Bata dago kanta ba har lkcn, hannu ya kai shoulders dinta ta ja baya da sauri ta fashe da kuka sosai, yyi shiru yana kallonta, ta hade kai da gwiwa ta dinga rerawa, dafe kansa yyi ya lumshe ido, can ya dago a hankali ya mike ya isa dab da ita xai dagota tsaye, ta fara turasa tana cewa "Plss ka bar ni, baxan iya ba" ya xaunar da ita gefen gado da damuwa yace "Believe me wife, kinsan if i was on my senses baxan maki haka ba, i won't hurt my wife this much, i will never hurt you, don Allah kiyi hakuri ki yafe min, it wasn't intentional plsss" kuka kawae take, rungumeta yyi ya lumshe ido cikin sanyin murya yace "Ina son ki Samha, i can't just come to you like that.... I won't hurt you knowingly" bata ce komai ba sae kukan da take, ya dago kanta ta ki bude ido, yace "Tell me ina ke maki ciwo yanxu plss" bata bude idon ba bare tace komai, ya langwabar da kai yace "Plss ki gaya min wife" kafarta ta nuna masa a hankali har lkcn idonta a rufe, ya lumshe ido ya daura hannu gashinta yace "Xai daina very soon, me xa ki ci?" Ta girgixa masa kai kawai, yace "A'a you have to eat sai ki sha magani.... Let me get you something now" yana saketa ta koma ta kwanta a hankali, ya mike ya fita daga dakin, sae da ya fara sllh a masallaci snn ya siyo mata gasasshen kaji da fresh milk sai take away na fried rice, yana shigowa compound mai aikin Ummi ta nufesa da leda hannunta ta mika masa tace "Wai Madam tace a kai maka" karba yyi ya wuce, yana shiga parlor ya bude ledan yaga magunguna ne da allura ya wuce daki, ya ajiye abincin hannunsa ya xauna gefenta yace "Ta shi dear ki ci abincin sai ki sha magani" bai jira cewarta ba ya dagota, haka ya sa ta gaba tana cin abincin da kyar, duk wani tausayinta ya dinga ji har ransa, gashi taki barin su hada ido, bai yi tunanin xata ma kula sa ba so soon bare ta ci abinda xae bata, sai kallonta yake ganin har ta fada sai idanuwanta da suka fito, lips dinta yyi ja sosai, tura abincin tayi ta jinginar da kanta da gado yace "Noo ki kara kadan plss baby" bata ce komai ba ya dau spoon din ya debi abincin ya kai mata baki ta kauda kai a hankali, da kyar ya lallabata ta sha milk din sai dai duk taki yrda su hada ido har lkcn, ya fara hada alluran bayan ya bata maganin ta sha, yace "Injection baby" kamar xata yi kuka tace "Baxan iya ba" yace "A'a xa ki iya mana dear, it's just two, baxan yi da xafi ba" daga haka ya daga ta yi rub da ciki kan gado yyi mata allurorin, ya dawo gefenta yana kallonta ganin yanda ta runtse ido yace "Sorry wife" juyar da kanta tayi xuwa daya side din, ya d'an yi murmushi ya jinginar da kansa da gado yana kallonta. Da daddare a bedroom dinta ya hada ruwan xafi a bayi, ya fito yana yace "Baby, you need hot water don kafar ya daina" a karon farko knn da ta kallesa da sauri tace "Ummi ta min daxu" a tsorace tayi maganar, yace "Tun safe ne ai" ta mike xaune ta fashe da kuka don bata mance ynda ta ji daxu ba tace "A'a ni bna so, ya daina min tun daxu" ya langwabar da kai yace "Toh bari in kirata ta maki dama ita ce tace xata xo nace ta bar shi" kuka sosai take tace "Toh ae ta min da safe" ya dagota yace "Ae ruwan fa ba xafi mu je ki taba, it's just lukewarm water" sae da ta sa ya salance ruwan gaba daya yana biye mata snn ta yrda ta cire kayan jikinta, kmr warce ta tuna abu tayi kasa da sauri tace "Ae xan iya da kaina" yace durkusa shi ma kusa da ita yana kallonta yace "What are u hiding?" Dauke kanta tayi tace "What am suppose to hide" dariya ta basa, yace "Aiitt bari dai in kira mamin kawai, ita ae u won't hide anything frm her" mikewa tayi da sauri, ya mike shi ma yana danne dariyarsa, da kansa ya karasa cire mata kayan, sai ta tsiri rufe ido, yana murmushi yasa ta shiga ruwan, da kansa ya wanketa, har lkcn idonta a rufe yake, ya kai bakinsa a hankali kusa da nata, da sauri ta bude ido jin saukar numfashinsa a fuskarta, ya lumshe ido ya shiga kissing dinta hannunsa a gashinta, kasa hanasa tayi sai kallon dogon hancinsa take, ya bude idanuwansa a hankali suka hada ido, da sauri ta rufe nata idon, ya xame bakinsa a hankali ya daura kan wuyarta, turasa tayi kmr xata yi kuka, ya mike da lumsassun idanuwansa ya dau towel ya mika mata yana kallonta, karba tayi ta mike ta daura har lkcn bai daina kallonta ba, ji tayi kawai ya dauketa sun fita bayin, ya xaunar da ita gefen gado ya durkusa gabanta ya kamo hannunta yana murxawa a hankali yace "Am proud of you wife..." Ko kallonsa bata yi ba, ya mike ya xauna gefen gadon ya kai bakinsa kunnenta yace "You made me feel complete yesterday...." Barin wajen tayi ta hade rai, yyi yar dariya ya mike ya fito mata da rigar bacci da undies, duk ynda ya so ta bari ya sa mata bata yrda ba, sai ya koma gefe ya xauna yana kallonta with passion, danna bell aka yi ya mike ya fita, fatima ce bakin kofar hannunta rike da warmer, ta d'an yi murmushi tace "Good evening" juyawa yyi ya bar gun ya nufi cikin parlor yace "Evening" bin sa tayi da kallo sai kuma ta bi bayan tace "Ummi told me she's sick, ga shi tace a kawo mata" ya nuna mata center table yace "Drop it da sauki" ajiyewa tayi ta kallesa tace "Can... I see her" bedroom ya nuna mata, ta d'an yi jim, da kmr ta fita kawai sai kuma ta nufi dakin, tsaye ta sameta, Samha ta juya tana kallonta, "ya jikin?" Cewar fatima tana kallonta ita ma, Dauke kai tayi tace "Na ji sauki ai" juyawa fatima tayi ta fice daga dakin ba tare da ta kallesa ba tayi kofar fita tace "Good nyt" yace "Nyt" mikewa yayi ya wuce daki. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 68..... Har ta gama sanya kaya kafin ya shigo dakin, ta wani daure fuska ta kwanta hade da juya masa baya, gefenta ya xauna yace "Ba gashi you re much better ba yanxu da kika yi wanka" bata juyo ba kuma bata ce komai ba, ya mike yace "Mami brought you something, let me check what's it" daga haka ya fita, ba a dau lkci ba ya dawo rike da warmer din da plate da cokali a hannunsa, ya ajiye k'asa yana kallonta yace "pepper soup, it's Yummy...." Ya bude warmer din yana kallonta, bai jira tace komai ba ya dibar mata pepper soup din kayan ciki ya mike yana rike da plate din ya xauna gefenta yace "Here it is" ta girgixa kai tace "Baxan ci ba" ya buda ido yace "Why?" Ta dauke kai tace "Na koshi" yace "Noo pls ki ci ko kadan ne, Mami ce fa ta aiko maki, kila ma ita tayi maki da kanta" daga haka ya ajiye plate din ya dagota, haka ya dinga bata tana wani yamutse fuska, ya kai daya baki yace "But it's sweet fa baby" bata ce komai ba, ya dinga forcing dinta ta ci me dan yawa snn ya kyaleta, sauka tayi daga kan gadon yace "Ina xa ki" nn ma bata ce komai ba ta wuce bathroom ya bi ta da kallo kafin yyi murmushi, brush ya ji tana yi, ya rufe sauran naman ya ajiye gefe, tana fitowa ta kwanta, ya matsa kusa da ita murya can kasa yace "Naga kafar ya kusa daina ciwo gaba daya koh?" Bata ce komai ba sai rufe idonta da tayi, yyi murmushi ya mike ya fitar da warmer din, sai da yyi wanka yayi shirin kwanciya kafin ya koma dakin ya tarar har tayi bacci, kashe wuta yyi ya kara A.c ya kwanta kusa da ita ya kai hannunsa fuskarta, farkawa tayi ta mike xaune da sauri, tana ganinsa ta fara kkrin sauka kan gadon ya rikota, ta fashe da kuka tace "Noo plss" jawota yyi ya kwantar da ita yace "Ni ba abinda xan maki fah baby kiyi baccin ki...." Ta kuma mikewa cikin rawan murya tace "Ni ba bacci nake ji ba" ya d'an yi murmushi yace "Do you want to sleep alone?" Kai ta gyada masa, yace "Alryt dear," daga haka ya sauka kan gadon yace "Toh kwanta" a hankali ta koma ta kwanta, ya rufa mata duvet, ya daura lips dinsa kan nata murya can ciki yace "I love you wife" light kiss yayi mata yace "Sleep tight baby" daga haka ya nufi kofa ta bi sa da ido har ya fita ya rufe mata kofar. Washegari wajen karfe bakwai ta tashi, ji tayi gaba daya bbu inda ke mata ciwo, ta sauka a hankali kan gadon ta nufi bathroom. Karfe bakwai da wani abu ta fito parlor ta gansa kwance yana bacci a 3 seater, kallon takardun dake kan center table a gabansa take kafin ta karasa ta dauka, kallo daya tayi ma uban rubutun da yyi ta hade gaba daya ta yaga in to three ta ajiye masa nan kan table din ta juya ta koma daki, ringing din wayarsa ne ya tada sa, ya jawo wayar a hankali yana kallon screen din ya ga Small mum dinsa ce, mikewa xaune yayi ya daga ya kai kunne, amsa sallamarta yyi yace "Mum!" Tace "an tashi lfya?" Ya gaisheta ta amsa tace "Kai baka kiran mutane Aliyu" ya shafa kai yace "Kiyi hakuri sweet mum, sometimes ina tunanin kiran is nt safe" tace "Alryt, ina ku ke a gombe?" Shiru ya d'an yi sai kuma yace "Na'am" tace "You heard me right Aliyu" murmushi yyi yace "Mum xuwa xa kiyi?" Tace "Ko kar in xo?" Ya wara ido yace "Noo, mum you re welcm.... Yaushe xa ki xo plss?" Tace "Gobe Saturday in'sha Allah" yace "Waoww, Allah ya kai mu mum, but please kiyi persuading Mami ta bar su ilham ku xo tare, am really missing them" tace "I think ur dad is around" shiru yyi bai ce komai ba, tace "Amma kayi mata flashing, idan ta kira sai ka tambayeta ka ji me xata ce" yace "Toh mum i will do that right away" tace "Alryt" yace "Let me send u the address ynxu" sallama suka yi, yyi texting mata address snn yayi ma Mami flashing, Mami dake bedroom dinta tare da su Ilham ta dau wayarta tana kallo, duk da ba saving din number tayi ba tasan wanda yyi flashing din, kira tayi ta kai kunne, yana dagawa tace "Aliyu" yace "Ina kwana Mami" tace "Lfya lau, ya kuke?" Tuni su Ramla suka dawo kusa da ita gaba daya ko wacce na son a bata waya, daga daya bangaren yace "Mami pls pls kiyi convincing Abba ya bar su Ilham su taho tare da Mum..." Kamar xae mata kuka yyi maganan, tace "Makarantar fa Ali?" Yace "Mami bai fi su yi sati daya kawai ba fa" shiru tayi... Yace "Plss Mami" tace "Toh bari in ji yanda xae ce" da sauri yace "Amma Mami ina xa ki ce masa za su?" Tace "Gidanku!" Murmushi yyi yana shafa kansa yace "When shud i be expecting ur call Mami" tace "Sai mun yi magana da shi" yace "Toh nagode Mami" tace "Ina matar taka?" Ya kalli agogo ganin tara ya wuce yace "Tana gida" tace "Kai kana ina?" Yace "Emm na fito gun aiki" tace "Alryt" daga haka suka yi sallama dai dai lkcn da idonsa ya sauka kan takardun kan table, mikewa yyi da sauri ya daukesu yana kallo da mamaki, can ya kalli hanyar bedroom ya kuma kallon takardun, bedroom din ya nufa ya bude dakinta, gyaran gun kayanta ya sameta tana yi, ya karasa cikin dakin yace "Why did you tear this Samha?" Bata ko kallesa ba tace "Why did i tear what??" Shiru yyi yana kallonta, jin bai ce komai ba ta juya ta kallesa, kallonta taga yana yi ta turo baki ta ci gaba da abinda take yi, yace "Kin san meye wnn din kika yaga?" Ba tare da ta kallesa ba tace "Yea, ko ba assignment ba" ya girgixa kai yace "Noo, it's research da Mami ta bani in yi, nd i have being doing this tun shekaranjiya a office, i completed it around 3am this morning nd you've ruined everything" juyawa tayi ta kalli takardun, ya juya ya bar dakin ta bi sa da ido, a hankali ta juya ta ci gaba da abinda take yi, tana gamawa ta fita daga dakin, kitchen ta wuce ta kunna gas ta daura ruwan lipton ta xuba kayan kamshi snn ta fara feraye Irish, cikin minti talatin ta gama hada breakfast ta kai parlor ta ajiye, bedroom dinsa ta nufa ta tura kofa a hankali ta shiga, tsaye ta gansa ya gama shiryawa cikin fararen shadda, ya dau makullin mota da takardun ya juya suka hada ido, ta hade rai tace "Toh ni ban san it's useful ba ai, am sorry" yace "It's ohk" daga haka ya nufi kofa ta bi sa da kallo, can ta bi bayansa, har ya kai kofar fita tace "Baxa ka yi breakfast ba?" Ya bude kofar yace "Ki ci nawa da naki" daga haka ya fita. Karfe sha daya Mami ta samu Abba a part dinsa, ta xauna tana kallonsa tace "Col, Mariya xata je yola gobe, ina son ta je da su Ramla su gaisa da gwaggwo da yan uwana, rabonsu da can kusan shekara bakwai" idonsa na kan takardan hannunsa yace "Boko da islamiyyan fah?" Tace "Ae yau friday, bai fi su yi kwana uku ba, ran Monday ko talata xa su dawo" ya girgixa kai yace "Noo, it's better a bar shi lkcn hutu Madam" tace "Amma ae baka cewa sae lkcn hutu xa su gun yan uwanka col, duk lkcn da kayi ra'ayi kke cewa su shirya su je, kayi adalci mana Yallabai, sorry to say, yan uwa fa ba su fi yan uwa ba" sai a snn ya kalleta yace "Su nawa xa su bi ta?" Tace "Su duka" wani kallo yyi mata yace "Kin taba ganin inda aka tura yara gaba daya lkci daya suyi tafiya, kinga ki bar ni in ci gaba da ji da rashin Ali...." Ta buda ido tace "Toh fah! Rashin sa na damun ka kenan?" Yace "Did you knw what an only son means?" Ta d'an yi murmushi tace "I never thought u were missing him, har ina mamakin duk bond din ka da Aliyu ka iya watanni da dama ba shi tare da kai, bana manta lkcn da yake karatu waje, kusan duk karshen wata biyu ana kan hanyar xuwa gun only son" wani kallo ya watsa mata yace "Are you teasing me?" Tace "Why will i.... nasan duk inda Abuturrab yake he is also missing home, just that he knws d kind of dad he has, am pretty sure he is afraid of coming back, baxae taba dawowa ba kwana kusa na sani" ya mike ya kuma jefa mata wani kallo yace "Ki fadi alkhairi ko kiyi shiru" daga haka ya nufi kofa, ta bi sa da ido tana murmushi, can ta mike da sauri tace "Col ya maganar tafiyar su Ramlan" yace "yarana baxa su bi hanya gaba dayansu ba, sai dai daya ta bi ta" ta girgixa kai tace "Ba wannan xancen, sai dai Ilham da Khaleesat su bi ta ita Ramla ta hakura" bai tanka ta ba ya fice. Abuturrab na xaune office ya kira small mum dinsa, tana dagawa suka gaisa yace "Mum kinsan me, pls ina son ku taho min da motata ne wllh" ta bude baki tace "A kai xa mu dauro motar?" Dariya yayi yace "Nooo Mum, driver xa ku yi hiring yayi driving din har gombe" ta tabe baki tace "That's if it's going to be possible son" daren ranan Ilham da Khaleesat driver ya kai su gidan Hajiya Mariya cikin motar Abuturrab bayan tayi ma Mami bayanin ynda suka yi da shi kan cewar a taho masa da motarsa, ba motar kadai ba har wasu daga kayayyakinsa sai da Mami ta hada ta sa a Booth din motar har da laptops dinsa biyu, snn tayi masa dambun nama me yawa, Ramla bata wani damu ba don bata san gun yayansu kannin nata xa su ba, su kansu basu sani ba kawai dai Mami tace masu yola xa su tafi da Hajiya Mariya. Bayan isha Abuturrab ya dawo gida, wanka yyi ya canxa kaya ya fito, tsaye yyi bakin kofar dakinta na kusan minti biyar kafin ya tura kofar, xaune ya ganta can karshen gado ta jinginar da kanta da gadon tana sanye da kayan bacci, ya rufe kofar ya karasa kusa da ita yace "Na xo da wasu takardun saura ki kuma yaga su Madam" bata ko kallesa ba, yace "Au ni bn yi fushi kin bata min aiki ba sai ke da kika yi barnan?" Kkrin sauka take daga kan gadon ya jawota ya kwantar da ita kan gadon yace "Xan yi maganin ki ynxun nn yarinya" ja baya ta fara yi da sauri ganin rigarta yake son ya cire tace "Meye haka doctor, bana so...." Bata rufe baki ba ya fara kiss dinta, iyakar tsorata tayi a lkcn ganin abinda yake mata, ta fashe da kuka tace "Na shiga uku, Allah xan mutu ne doctor, ka kyaleni pls kayi hakuri baxan sake ba na rantse maka" Sai da yaga numfashinta na neman daukewa snn ya kyaleta, ko second biyar bata kara kan gadon ba ta mike jiki na rawa xata sauka yyi saurin riketa, ta kuma fashewa da kuka cikin rawar murya tace "Wayyo doctor am begging you kayi hakuri" mayar da ita yyi ya kwantar yana kallonta da idanuwansa da ya sauya kala yace "Sleep" rufe idon tayi da sauri har lkcn jikinta na bari, kwanciya yyi shima ya jawota jikinsa, xata fara kuka yyi mata alamar tayi shiru, ba shiri ta hadiye kukan, suna nn a haka har bayan minti goma, a hankali taji yace "Kin ci abinci?" Ta gyada masa kai da sauri, yace "Sure?" Nn ma kai ta gyada mai, a hankali ya kai bakinsa kunnenta yace "Baby bbu fa abinda zan maki, just want to play with you, i promise i won't pass that" ta fashe da kuka sosai yace "Plsss wife" tana ji tana gani ya mayar da ita yanda yake so gabansa, ba a jima ba tsoron ya saketa gaba daya, bata kuma hanasa abinda yake ba, sai da yaga tayi likis ya kyaleta ya shiga bathroom, lkci daya bacci ya dauketa. Har ya dawo daga masallaci da Asuba bacci take, ya xauna gefenta ya tsura mata ido, komai nata is just different and special, he can't wait knowing her for the second time, ya sauke idonsa kan dogayen kafarta masu taushi da haske sosai, hannu ya kai kafar ta bude ido a hankali, suna hada ido ta kauda kai da sauri, yyi murmushi har lkcn hannunsa na kan kafar yana shafawa cikin magana irin tata yace "Doctor stop pls, stopp, doctor Wait...." Yar dariya yyi yace "And she likes it so much fahh, she's enjoying it" yana fadin haka ya mike ya leka fuskarta yaga murmushi take suna hada ido tayi yar k'ara ta boye fuskarta jikin pillow ta dukunkune waje daya, dariya yyi ya fita daga dakin. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 69..... Tana daure da towel ya shigo dakin, tayi masa kallo daya ta mirror ta ci gaba da abinda take, ya isa bayanta ya d'an duka dai dai fuskarta yace "Shud i help?" Bata fuska tayi ta girgixa masa kai, ya ja hancinta yace "You love pretending" tashi take son yi daga wajen yaki barinta tace "Shiryawa xan yi fa doctor" yace "But am nt stopping u nurse" bata kuma cewa komai ba, ya daura hannu gashinta yana shafawa yace "Kin san me wife?" Ta madubi ta kallesa, ya wara mata ido yace "My small mum nd siblings will be coming today in sha Allah" juyawa tayi ta kallesa tace "Da gaske?" Yace "Yea dear, har sun taso" tace "Toh Allah ya kawo su lfya, what will i be cooking for them?" Yace "Abinda kika ga ya dace" tace "Ohk, xan yi shinkafa da miya with cow meat, sai inyi tuwo da miyar vegetable with meats also, i will make them xobo nd ginger drink, sai inyi coslow.... With a little pepper soup" yace "Duk ke kadai?" Tace "Eh mana xan iya ai" yace "Toh wa xai je kasuwa" tace "Kai mana" yace "Ni kuma, noo i can't just go the market nd start pricing meat, i only knw how to go to supermarkets to get foodstuffs" dariya tayi yace "Yea baby, sai dai mai aikin Mami ta raka ki ku je, xaki fi sanin duk abinda kike bukata" tace "Tohm" yace "Bari in fadi ma Mami my mum is coming" daga haka ya manna mata kiss a wuyarta ya fita daga dakin. Fatima ce kadai ya gani parlor a kwance handout a hannunta, yana kallon mai aiki yace "Ummi na ciki?" Ta kalli fatima tace "Eh, sai dai tayi maka magana da ita a daki" Sai a snn ya kalleta suka hada ido, ta mike xaune tace "Ina kwana" yace "lafiya lau" Mai aikin tace "Madam yake nema wai" ta gefen ido ta watsa mata wani kallo, can ta mike, jeans ne jikinta da top, ta dau hijab dinta ta sa ta wuce daki, dauke kansa yyi daga kallonta ya nemi kujera ya xauna, ba a dau lkci ba Ummi ta fito, ya gaidata da ladabi ta amsa tace "An tashi lfya boy" yace "Alhmdllh Mami," tace "Toh ya aka yi, ko wani Malaria typhoid din take yi kums?" Sunkuyar da kansa yyi yana murmushi, sai yaji nauyinta ba kadan ba, ya kawar da xancen yace "Mami dama mum dita da sisters dina ne xa su xo yau, shine na xo in gaya maki" tace "Ayya, that's nyc, Allah ya kawo mana su lfya, daga kano xa su taho knn?" Yace "Eh Mami" tace "Toh Allah ya tsare hanya" yace "Kuma Mami wai kasuwa zata tana son mai aikin ki ta rakata" tace "Har ta warware ne da zata fita" yace "Ta ji sauki Mami" tace "Toh shknn, sai su je, fatima tayi masu driving din" yace "Toh Mami, thank you" tace "You took pills for a virgin sbda rashin imani koh?" Bai zaci maganan nata a lkcn ba, ya kasa dago kai yace "Ba haka bane Mami" tace "Toh ya ne" yana shafa kai yace "Mami bn san ynda ya faru ba" tace "to ae ka kyauta" Mikewa tayi tace "Alryt bari in yi fatima magana ta shirya sai su je" yace "Toh nagode Mami" daga haka ta shiga ciki, shi kuma ya fita, yana xaune balcony mai aikin Ummi ta iso gun ta gaishesa tace "Samhan ta shirya?" Mikewa yyi ya shiga ciki, ba a dau lkci ba suka fito tana sanye da hijab ta rataye jaka, yana kallonta yace "Baby baxa ki koma ki sa nikab ba kuwa?" Ta d'an kallesa ta dauke kai tace "No" daga haka ta kalli Usaina tace "Mu tafi" Usaina ta bi bayanta suka bar gun, yyi murmushi ya koma ya xauna. Fatima na mota tana jiransu, Samha ta bude gaban motar ta xauna, Usaina ta xauna a baya, hada ido suka yi da fatima ta sunkuyar da kai tace "Good morning" can ciki fatima tace "Same" snn ta tada motar. Suna isa kasuwan Usaina ta fara fita kafin Samha, Fatima ta kwantar da kujeran motar ta sakala earpiece tana kallon Usaina tace "Kar a bata min lkci ina da abun yi me muhimmanci" Samha ta kalleta tace "It's ohk, kiyi wucewar ki akwai abun hawa" kallonta kawai fatima ke yi, ta juya ta bar gun Usaina ta bi bayanta, Minti talatin suka yi a kasuwan ta siya duk abinda tasan xata bukata snn suka fito, bata yu mamakin ganin wucewa fatima tayi ba, tana kallon Usaina tace "Mu samu adaidaita mu wuce" hakan aka yi, suna isa gida, Abuturrab yace "Ina fatimar?" Wani kallo Samha tayi masa tace "How wil i knw" daga haka ta shiga ciki, har ta fara girkin Usaina ta xo wai Ummi tace ta taya ta. Sai kusan sha daya da rabi suka gama komai, ta dibar ma Ummi ta ba Usaina ta kai mata ta kuma ce ta dawo ta karbi nata. Hajiya Mariya na ganin sun iso gombe kawai ta sallami drivern ta basa dubu 30, sai dubu goma kudin motar da xae mayar da shi kano, daga nn ta karbi driving din, Abuturrab ya dinga yi mata kwatance a waya, da yake tana yawan xuwa gombe don nn yan uwan mijinta suke, gane wajen bai mata wahala ba, ko da wasa su ilham basu kawo da wanda take wayan ba, Ilham tace "Mum wai ina xa mu, i thought yola xa mu at the 1st place...." Hajiya Mariya tace "Toh ki sauka ki tafi yolan" dariya tayi tace "A'a ni fa bn ce haka ba Mum" Khaleesat dai sae ture turen baki take, dai dai number gidan da Abuturrab yace ta tsaya ta tsaya tayi horn, mai gadi ya bude gate din, yana tsaye kusa da balcony ta shigo da motar, Ilham ta juya a hankali ta kalli Khaleesat ganin wanda ke tsaye compound din gidan, wani k'ara khaleesat ta saki tana son bude motar tace "Yayanmuu...." Hajiya Mariya bata gama parking ba ta bude masu motar kawai suka fice gaba daya, Buda hannayensa yyi ya lumshe idonsa suka nufesa da gudu, lkci daya suka fada jikinsa ya rungumesu, duk suka fashe da kuka, Ilham tace "Why did you leave us ya Abuu, me yasa ka tafi ka bar mu" lips dinsa ya daura a forehead dinta yace "Ban bar ku ba Lil sisters," ta kuma saka wani kukan tace "We missed u yayanmu, don Allah ka xo mu koma gida plss" share hawayen idonta yayi yana murmushi yace "Toh ba gashi kun gan ni ba ilham" kallon khaleesat yyi, ta fashe da kukaz ya ja hancinta yana murmushi yace "Kuna son nima in fara kukan ne" Duk wnn abun Samha na tsaye balcony tana kallonsu, duk jikinta yyi sanyi ta kasa karasowa, janye kannin nasa yyi jikinsa ganin small mum dinsa tsaye tana kallonsu tana murmushi, ya karasa inda take ya rungumeta yace "Welcome sweet mum" shafa kansa tayi tace "Thanks Son" daga Ilham har Khaleesat kallon Samha dake tsaye balcony kawai suke, ta sunkuyar da kanta tana wasa da yatsunta, can ta sakko a hankali ta nufo su, har ta iso inda suke idonsu na kanta, da kyar tana murmushin dole tace "Sannun ku da xuwa" Khaleesat ta juya mata baya, Ilham kadai tace "Thanks" ita ma ta juya, sosai jikinta yyi sanyi, ganin sun hada ido da Hajiya Mariya ta karasa inda take jikinta duk a mace, ta d'an risina tace "Sannu da xuwa mum" jawota Hajiya Mariya tayi ta rungumeta tace "Thanks Daughter, da fatan mun same ku lfya?" Juyawa Abuturrab yyi ya nufi sisters dinsa ya kama hannunsu ya nufi ciki da su, Ita kuma Samha suka taho tare da Hajiya Mariya dake rike da hannunta, har kasa samha ta durkusa ta gaida Hajiya Mariya bayan sun shiga ciki, ta amsa mata da fara'arta, kallonsu Ilham dake gefen yayansu tayi ta gaishesu su ma, Ilham tace "Lafiya" khaleesat kam ko kallon inda take bata yi ba, Hajiya Mariya bata ji ddin hakan ba sai dai bata ce komai ba, Shi kansa Abuturrab har cikin ransa yaji hakan da suka yi mata, sai dai shi ma bai nuna ba, ita kam mikewa tayi a sanyaye ta kawo masu ruwa da Exotic drinks ta ajiye masu, Hajiya Mariya ta diba ruwan ta sha tana kallonsu ilham tace "Baxa ku sha ruwan ba" bata jira cewarsu ba ta mike tana kallon Samha tace "Daughter xan yi sllh" mikewa Samha tayi ta kai ta har bedroom dinta ta nuna mata bathroom, Abuturrab ya dibar ma kannin nasa drink din da kansa ya basu suka karba, yace "Me yasa Ramla bata biyo ku ba?" Khaleesat tace "Mami tace ita ta tsaya, we never knew we were coming to see you brother" marairaice masa tayi kamar xata yi kuka tace "Don Allah don annabi yayanmu mu tafi gida tare we all missed you, more especially mami" daga haka ta fashe da kuka, ya rungumeta yace "Xan dawo sis but ba yanxu ba, am still nt ready for the punishment...." Ilham ma ta saka kukan tace "We so much miss you ya Abuu..." Rungumeta yyi ita ma yana murmushi yace "Toh ba gashi kun gan ni ba" *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 70..... Samha ta fito parlorn tana kallonsu a hankali tace "Baxa ku yi sllhn ba ku?" Khaleesat ta juya ta kalleta a takaice tace "Idan xa mu yi ae xa mu tashi" Abuturrab ya kalli kanwartasa sai dai bai ce komai ba, juyawa Samha tayi tace "Toh" snn ta bar wajen ta nufi kitchen, abinci ta shiga daukowa tana ajiye masu a parlor, ta dauko har da plates, spoons da cups, rasa ynda xata ce masu ga abinci tayi, tana nn durkushe har kusan minti uku a wajen, gaba daya hankalinsu na kan wayar Ilham dake hannun Abuturrab ko me suke kallo, fitowar Hajiya Mariya yasa ta mike tsaye, tana xaunawa kuwa tace "Mumy ga abinci" Hajiya Mariya tace "Toh sannu daughter, Allah yayi albarka" sai a snn duk suka kallota, komawa tayi ta duka ta bude warmer din abincin, ta dibar ma Hajiya Mariya, snn ta kalli su Khaleesat tace "In xuba maku ko xa ku xuba da kanku?" Dauke kai khaleesat tayi ta mayar da hankalinta kan waya, Ilham tace "No thanks" rufe warmer din tayi, ta xuba ma Hajiya Mariya miyan a waje daban, ta dibar mata coslow, duk ta kai mata gabanta har da drinks din, ta dago da kyar tace "Mumy akwai tuwo...." Hajiya Mariya tace "Bari in ci shinkafar tunda kin xuba" kai kawai ta gyada mata ta mike a hankali xata wuce daki taji khaleesat na cewa "Yaya ni take away nake so" Hajiya Mariya tace "Take away kuma?" Tace "Eh" Abuturrab yace "Ba ga abinci ba leesat" girgixa kai tayi tace "I prefer may be chips nd sauce" d'aga kafada yyi yace "Ohk" Ilham tace "Ni kuma jollof rice with plantain nake so" Hajiya Mariya tace "Allah xan yi maganin ku idan baku shiga hankalinku ba...." Abuturrab yace "Mum ki bari in siyo masu abinda suke so mana" Wani kallo ta watsa masa ya mike yana murmushi, Samha ta karasa shiga dakinta ta kwanta kan gado, hawaye taji na sakko mata ta dinga gogewa amma yaki tsayawa kawai ta hade kanta da pillow tayi kukan ko xata ji dadi, bude kofar dakin aka yi, yana tsaye daga bakin kofa yace "Dear ina Atm card dina?" Ba tare da ta dago ba ta nuna masa jakarta, ya karasa gun jakar ya bude ya dauka yace "I will be right back" daga haka ya fita, ta kuma fashewa da kuka, Yana isa parlor su Ilham suka ce xa su bi sa yace duk su je, sai bayan kusan minti talatin suka dawo gidan, duk suka wuce ciki da ledoji a hannunsu, shi kuma ya nufi part din Ummi, tana parlor ya sameta bayan ya gaisheta yace "Mami sun iso, i came to check ko kina nn ne, so i can bring my mum here" tace "Noo su da suka sha hanya, don't worry xan shigo yanxu" yace "Toh shknn Mami sai kin shigo" daga haka ya bar parlon, Xaune ya tadda su Ilham har sun fara cin abincin su, Hajiya Mariya kuma na waya, ya karasa bedroom din Samha, ganinta kwance ya isa kusa da ita yace "Baby bacci kika yi" rufe idonta tayi da sauri, ya leka fuskarta yace "Baby ki koma bedroom dina so as my mum will rest here, su Ilham kuma sai su yi amfani da other room din" bata bude ido ba bare ta ce masa komai, ya juya ya fita, mikewa tayi bayan kusan minti goma ta kuma gyara gadon, ta kunna burnern turare ta dau abinda xata bukata ta fita daga dakin ta koma other room din jin sa da kanninsa a bedroom din nasa da yace. Ba a dau lkci ba Ummi ta shigo parlon, kallon Hajiya Mariya ta dinga yi har ta xauna snn suka gaisa da fara'a har lkcn bata daina kallonta ba tace "Wllh gani nake kamar na san ki" Hajiya Mariya tayi dariya tace "Anya kuwa" Ummi tace "Ehh wllh, kamar mun taba haduwa shekara daya knn a Umrah" Hajiya Mariya tace "Kuma gashi bn yi Umra shekarar da ta wuce ba" Ummi tace "Ikon Allah.... Ae kam kuna kama sosai ita wancan sunan mu daya ma" Hajiya Mariya tace "Ya sunan?" Ummi tace "Hajarah" Dariya Hajiya Mariya tayi tace "Ahaf, to kilan yayata ce, Mahaifiyar Aliyu" Ummi ta bude baki tace "Mahaifiyar Aliyu, ae har gobe muna gaisawa da ita a waya muna chatting" Hajiya Mariya tace "in ga number nata" Ummi ta fiddo number a wayarta dake hannunta ta mika ma Hajiya Mariya, dariya sosai Hajiya Mariya tayi tace "Wllh ita ce, yayata ce uwar mu daya ubanmu daya, ita ce kuma ta haifi Aliyu" Ummi da mamaki ya cikata tace "Ikon Allah, Allah mai girma, kuma wllh ranan da na fara ganin Aliyu ita ce ta fado min ganin suna kama, sae dai bn kawo komai a rai ba...." Hajiya Mariya ta kira Abuturrab ya fito ganin Ummi yace "Har kin shigo Mami" Ummi sai kallonsa take tana murmushi, Hajiya Mariya tace "Kaga ashe tasan Mami ma sun hadu a Umra last year" kallon Ummi yayi ya xauna kusa da ita yace "Da gaske Mami, you know my mum" Ummi ta girgixa kai tace "Amma ko baka yi halin mum dinka ba Aliyu, matar so gentle, kai kuma you re nt" dariya yayi yace "What a coincidence, you have the name of my mum shi yasa nake ce maki Mami don haka nake kiranta" Ummi tace "It's nyc staying with my son all this while" ta kalli Hajiya Mariya dake ta dariya tace "Sai dai fa Aliyu bai ji...." Hajiya Mariya tace "Ae mu xa mu baki wnn lbrin" Mikewa yyi alamar bai son xancen ya bar masu parlon da sauri. Hira sosai Ummi da Hajiya Mariya suka yi, nan Hajiya Mariya ta dinga bata lbrin dalilin barin Abuturrab kani, Ummi tayi murmushi tace "He told me everything, Prayer is the best thing for him, sae dai ni inda yake burgeni duk abunsa yana da kamun kai, yana da addini, kinga duk xamansu da yarinyar nn kafin ya aureta bai yrda ya sa6a teachings din addininsa ba..." Hajiya Mariya tace "Ba fa xama waje daya kike da su ba Hajiya" Ummi tace "Noo ni nasan abinda nake ce maki, Aliyu is different" Hajiya Mariya tayi murmushi tace "Toh mu dai gashi har yau ya bari mahaifinsa na xarginmu" Ummi tace "Toh Allah ya kawo sassauci lamarin" Ummi ta dau wayarta tace "Bari in kira Namesake din tawa ynxu" Ummi na dialing number Mami ba a dau lkci ba ta daga, da fara'arta tayi mata sallama daga daya bangaren, Ummi ta amsa tace "Kuna lfya Hajiya?" Mami tace "Lafiya lau wllh, ya yarana" Ummi tace "Duk Alhmdllh, ya kano?" Mami tace "Gamu a cikinta, ya mai gidan ki" Ummi tace "Yana lafiya wllh, Hajiya ga ni ga kanwar ki" Mami tace "Kanwata kuma, a ina kenan?" Ummi tayi dariya tace "Ga ta ku yi magana" mikawa Hajiya Mariya wayar tayi ta karba tana murmushi tace "Hello Mami" Mami da mamaki ya cika ta tace "Toh fa, kinsan ta ne Mariya?" Hajiya Mariya tace "Gashi nasan ta yau ta dalilin Aliyu" Mami tace "Aliyu?" Hajiya Mariya tace "Shi fa, gidansu daya da shi, ita ce kuma wanda kika ce min ya taba baki lbrin ta" Mami tace "Ikon Allah, ae tare muka yi Umrah da ita last year" Hajiya Mariya tace "Haka ta ce" Mami da farin ciki ya lullube ta tace "Allah mai iko, bata wayar" mika ma Ummi wayar tayi, nan Mami ta fara mata godiya, Ummi tace "Haba ae d'an ki nawa ne Hajiya, it's nothing yi wa kai ne, mu dai muna xuba idon xuwan ki gombe soon" sun fi minti sha biyar suna magana daga bisanni Ummi tace "Wai dama Aliyun da kike cewa xaki hada da 'yar ki fatima knn" Dariya Mami tayi tace "Shine fa, kin kuma ga abinda ya xabar ma kansa, sae dai duk da haka ae bai baci ba" Ummi tayi dariya tace "A'a Samha ma 'ya ta ce Hajiya...." Mami tace "Ehh sai ya xauna da duk 'ya yan naki biyu" Dariya kawai Ummi take daga haka suka yi sallama ta katse wayar, sai kusan la'asar ta bar parlon bayan sun yi hira sosai da Hajiya Mariya, Abuturrab kam na bedroom dinsa a kwance da sisters dinsa, lbrin tun daga ranan da ya bar gida kawai suke basa, da irin abubuwan da Abbansu ya dinga yi, wani yyi dariya, wani ya xaro ido, muryar small mum dinsu suka ji a kansu suka juya gaba daya, tace "Ina Samhan take?" Su ilham suka dauke kai, ya mike xaune yace "Ina jin kmr tana daki" tace "Shine xa ku bar ta ita daya Aliyu?" *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 71..... Khaleesat tace "Lbri fa muke basa mum" harararta tayi tace "Did i ask for your opinion?" Mikewa Abuturrab yyi ya fita daga dakin ya wuce dakin Samha, ganin bata ciki ya juya ya fito, Hajiya Mariya dake tsaye tana kallonsa tace "Tana ina?" Kallon spare room yyi yace "Ina jin tana nan" daga haka ya karasa ya bude kofar ya ganta kwance, tana jin an bude kofa ta rufe ido da sauri, ya isa bakin gadon yace "Dear are you sleeping?" Bata tanka sa ba kuma bata bude ido ba, ya juya ya fita yace "Mum she's sleeping" bata ce komai ba ta bude dakin Samha ta shiga ya koma dakinsa. Karfe biyar da rabi Samha ta fito sanye da hijab ta shiga bedroom dinta, Hajiya Mariya ta katse wayar da take tana kallonta murmushi dauke fuskarta tace "Kin tashi daughter?" Samha ta kirkiri murmushi ta karasa inda take ta durkusa tace "Na tashi mum" Hajiya Mariya tace "Amma kin ci abinci koh?" Kai ta gyada mata tace "Na ci, dama xan tambayi me xan dafa maku ne" Hajiya Mariya tace "Ba kince akwai tuwo ba?" Samha tace "Eh akwai" Hajiya Mariya tace "Toh kar ki damu kanki xa mu ci tuwon" mikewa tayi tace "Toh" snn ta juya ta fita, parlor ta nufa ta kwashe duk kwanukan dake gun ta kai kitchen, shinkafa ta diba kadan ta sa stew ta ajiye a gefe, ta dau sauran shinkafar dake cikin warmer din ta xuba miya da coslow da ya rage a gefe, ta bude kofar kitchen ta fita ta kai ma mai gadi ta dawo, wanke kwanukan tayi ta sake gyara kitchen din ta goge ko ina snn ta dau shinkafar da ta diba da goran ruwa ta fita ta koma daki, duk yanda ta so cin abincin kasawa tayi, ta jinginar da kanta da gado tana kkrin mayar da hawayen da ya taru idonta, mikewa tayi a hankali ta isa gun window ta tsaya tana kallon waje. Dab da Magrib aka danna bell din gidan, Abuturrab ya tare da su Ilham yana bude kofar ya ga fatima ce tsaye da warmer biyu a hannunta, ya juya ya bar gun, khaleesat ta bi bayansa tace "Who's she, she's cute" Ilham ta karbi dayan warmer din hannunta tace "Welcome" fatima ta sakar mata murmushi tace "Thank you, kun xo lfya?" Ilham ta mayar mata da murmushin tace "Alhmdllh" daga haka suka karasa cikin parlorn, dukawa tayi ta ajiye abincin hannunta ta saci kallon Abuturrab taga kallonta yake, ta dauke kai tace "Good evening" yace "Evening" ta daga ma khaleesat hannu tace "Welcm" khaleesat tayi murmushi tace "Thank you" ta kalli Abuturrab tace "Mum fa?" Ilham tace "Ki shiga tana ciki" karasawa dakin fatima tayi, ilham ta kalli Abuturrab tace "Who's she Big bro?" Yace "Our neighbor" khaleesat tace "Ohk mum dinta ce ta shigo daxu?" Kai ya gyada mata, ta wara ido tace "She's cute, just like me" tabe baki yayi ya mike jin ana kiran magrib ya shiga toilet dake parlon, Ilham ta mike da sauri ta nufi kitchen don dauko plate da spoon, tana fitowa tace "As if she knws am very hungry" Khaleesat ma ta je ta dauko nata plate din, Abuturrab na fita masallaci fatima ta fito daga gun Hajiya Mariya, sallama tayi masu, ilham tace "The name?" Murmushi tayi tace "Fatima" ilham tace "I am Rabi'a but they do call me Ilham, and this is my sis khaleesat" Fatima tace "It's nyc meeting you all" khaleesat tace "Nyc meeting you too" fatima tace "Gobe ku shigo wajen mu pls" ilham tace "Sure, Allah ya kai mu" daga haka tayi masu sai da safe ta fita. Abuturrab na dawowa masallaci Ilham tace "Yayanmu gobe da safe xa mu shiga part din su fatima.... She's inviting us" bai tanka ta ba ya nufi bedroom, khaleesat tace "Ya Abuu?" Juyawa yyi ya kallesu, ta hade rai tace "Where r u goin to, magana fa ilham ke yi maka" yace "Ohh sorry, just 2mins ina xuwa" daga haka ya wuce dakin da Samha take ciki, xaune take idonta a kan magazine dake hannunta, ya isa kusa da ita ya xauna gefenta yace "Baby me yasa baki son ki saki jiki da siblings dina?" Bata dago ta kallesa ba ta girgixa masa kai kawai, ya amshe magazine din hannunta ya dago kanta yace "Baki son ku saba da su ne? kin ma ci abinci kuwa?" kai ta gyada masa, ya langwabar da kai yace "Ni ko abincin ba a bani ba dear" bata ce komai ba ta sauke idonta kasa, yace "Ki xuba min shinkafar am hungry" tace "Ya kare" ya buda ido yace "Ya kare kuma? But i saw the rice kuma su khaleesat basu ci ba ae" tace "Na bayar" yace "Wa kika ba?" Tace "Gate keeper" Shiru yyi yana kallonta, can yace "Alryt, tuwon fah?" Tace "Na mum kadai ya rage" da mamaki yace "Sauran fah?" Tace "Ba shi da yawa dama" kallonta kawai yake, can ya mike yace "ok then, let me get what to eat" daga haka ya fita, tare da su Khaleesat ya fita a motarsa, ta mike ta kai ma Hajiya Mariya abinci daki, Hajiya Mariya na kallonta tace "Me yasa ba ki bi su kun fita ba Samha?" Murmushi tayi tace "Ba komai Mum" Hajiya Mariya tace "Toh kin ci abinci?" Kai ta gyada mata tace "Na ci" "Toh xauna mu yi kallo a nn" cewar hajiya Mariya knn tana nuna mata gefen gado, a hankali tace "Toh" snn ta xauna. suna nn zaune ita dai ba sanin abinda ake a film din tayi ba ma, banda tunane tunane bbu abinda take, a haka aka kira isha, bayan kusan minti goma Hajiya Mariya ta mike ta shiga toilet ta dauro alwala ta fito ta gabatar da isha, har tara da rabi basu dawo ba, Hajiya Mariya ta kalleta ganin ta jinginar da kanta da gado tace "Kina jin bacci ne Samha" murmushi tayi bata ce komai ba, Hajiya Mariya tace "Toh tafi kiyi kwanciyar ki, sai da safe kin ji" ta mike tsaye cikin sanyin murya tace "Toh mum, sai da safe" daga haka ta nufi kofa, Hajiya Mariya ta bi ta da kallo cike da tausayinta ganin ba wani shekaru gareta ba, ita dai kawai yarinyar tayi mata ne har cikin ranta, kuma ta dau alkawarin in dai tana raye baxata taba yrda Aliyu ya toxartata ba ko ya walakantata coz her case is totally different, Samha na komawa daki bathroom ta shiga tayi wanka ta fito, tayi shirin bacci snn ta kwanta ta rufe jikinta da duvet, Dad dinta ne ya fado mata ta fashe da kukan da bata san dalili ba, tayi mai isarta daga haka bacci ya dauketa, sai kusan goma da rabi Abuturrab ya dawo gidan da kanninsa, Ilham ta kai ma small mum dinsu abubuwan da aka siyo mata snn ta shiga dakin yayanta, sai da suka gama cin abincin snn ya shiga wanka, su kuma suna kwance kan gado suna kallo a laptop, yana gama shiryawa ya xauna gefensu yace "Ain't you girls going to take ur bath" Khaleesat tace "Sai mun gama kallo" Bai sake ce masu komai ba, suna nn suna kallo har kusan sha biyu, ya mike yace "Am feeling sleepy, idan kun gama ku sa min laptop din a charge, good nyt" Khaleesat ta juya tace "A ina xaka kwana yaya?" Yace "Other room, you 2 shud use this room" ta ci gaba da kallonta tace "Alryt good nyt," ilham ma tayi masa goodnyt ya fita ya rufe masu dakin. Dakin da small mum dinsa take ya bude yaga har tayi bacci ya rufo kofar snn ya nufi inda Samha take ya bude kofar ya shiga ya rufe ya kashe wutan dakin ya kara Ac, xaunawa yyi gefen gadon ya kunna bedside lamp yana kallonta, can ya cire duvet din da ta lulluba yana kallon kayan jikinta, kashe lamp din yyi ya hau gadon ya birgina kusa da ita ya jawota jikinsa ya kai bakinsa wuyarta a hankali yace "Wife" farkawa tayi xata mike xaune yaki saketa yace "Kawai kinyi isolating kan ki daga mutane throughout today baby, what's wrong with you?" Ba karamin daurewa tayi ba na ganin bata saki kukan dake cin ta ba, ya juyo da ita ya rungumeta yace "Seems baki son mutane koh?" Hawaye ne ya cika idonta ta sa hannu tana sharewa, kawai jin bakinsa tayi cikin nata ta fara turasa ya ki sakinta ya kwantar da ita, duk ynda ta so kwatar kanta kasawa tayi, a hankali ya sassauta rikon da yyi mata jin shesshekar kukanta, murya can kasa yace "Plss wife, you won't feel any pain" jin taki cewa komai ya kai bakinsa kunnenta a hankali yace "plsss?" Nan ma bata tanka sa ba, hakan yasa ya ci gaba da abinda yake, pain din da ta ji a lkcn bai kai na 1st encounter dinsu ba amma hakan bai hanata kuka a hankali ba, kukan ta kuma bai sa ya sarara mata ba, rungumeta yyi daga karshe cikin sanyin murya yace "Am sorry baby, i just can't help" ita dai bata ce komai ba, yana rungume da ita har bacci ya dauketa. *Haske writers asso* Kar ya auri fatima, bai dace ya aureta ba, bai kamata ayi ma Samha kishiya ba, as if anji Abuturrab ya bude baki yace he have interest for fatima, as if har ya biya sadaki,🤔 Noo My Aliyu has taste don haka stop being faster than ur shadow fanz 😅😆 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 72..... Karfe hudu da rabi ya farka ya mike xaune yana kallonta, duvet ya jawo ya lulluba mata ganin kmr tana jin sanyi, ya taba jikinta yaji da dumi ya kafa mata ido yana kallo, can ya manna mata kiss a forehead ya mike ya shiga toilet don yin wanka, jallabiyansa ya xura jin xa a tada sllh ya fita masallaci, yana dawowa ya shiga dakin ya xauna gefenta ya kuma taba jikinta yaji ya fi daxu xafi, kallonta kawai yake kafin ya mike ya fita dakin, dakinsa yyi knocking ya bude ya sami sisters dinsa suna ta bacci, ya nufi gaban mirror ya bude a hankali ya dau alluran da xai dauka da syringe ya rufe gun snn ya fita ya koma daki, ajiye su yyi gefen gado ya shiga bathroom ya hada mata ruwan wanka ya fito ya xauna kusa da ita ya daura hannu forehead dinta, a hankali ta bude idonta don hannunsa da ruwa, kkrin tashi xaune ta shiga yi, ya dagota yace "Mu je kiyi wanka baby, you will feel much better" bai jira cewarta ba ya tashi tsaye ya daga ta ya wuce bathroom din da ita, bata yi xaton xata iya takawa ba don duk a tsorace take, duk ynda yaso taimaka mata tayi wankan kin yrda tayi hakan yasa ya fito ya barta, ta wanke baki snn tayi wankan, yana xaune gefen gado ta fito daure da towel ya bi ta da ido, can ya mike ya fita, kafin ya dawo har ta shirya cikin riga da skirt na atamfa ta kwanta, rike da cup din tea ya shigo dakin ya ajiye kasa ya xauna kusa da ita yace "Tashi ki sha tea sai in maki allura i don't want you to get sick" da kyar ta yrda ta mike xaune ta karbi cup din tea din, tana gama sha yace allura, nn hawaye ya cika idonta, bbu ynda ta iya haka ta tsaya yyi mata alluran, ya kwantar da ita yace "Toh yi ramuwar baccin ki" ko kallonsa bata yi ba, ya mike yana murmushi ya fita, gun small mum dinsa ya shiga ya sameta xaune kan darduma, ya xauna gefenta ya jira ta gama azkar din da take snn ya gaisheta, ta amsa tace "Jiya me yasa ba ku fita gaba daya da Samha ba Aliyu?" Ya kalleta yace "Mum, ae bata fiye son fita ba ita, kuma tana daki lkcn da muka fita" tace "Yanxu don ka ga yan uwanka sai ka janye mata Aliyu is that fair" da mamaki yace "Mum ba haka bane wllh, ynda kika ganta haka take, baka sanin abinda yyi mata da wanda bai mata ba, miskilancinta yyi yawa.... Ko magana ma sai taga dama wani lkcn, she will just be looking at you, ko da nace ta bi mu nasan cewa xata yi A'a" Hajiya Mariya ta tabe baki tace "Ni dai ina kara jaddada maka idan ka cuce yar nan Allah baxae bar ka ba, to wai idan baka dinga jan ta a jiki ba wa xai yi hakan Aliyu? bata da kowa fa a yanxu sai kai, gwara kai gun mahaifinka kadai kke da problem, ita fa? Duk duniyar nn ynxu da kai xata yi takama..." Ya d'an yi murmushi yace "Na sani mum, nd am trying my best to always be there for her...." Hajiya Mariya ta kuma kyabe baki tace "Amma da ai naga ba haka kke mata ba kafin ka rabata da iyayenta, ka fa kawota gidana na gani, duk da baka san tana da miskilancin ba ka iya lallabata har ka rabata da kowa nata, dama namiji in dai ya samu abinda yake so gun mace shkkn...." Kallon mamaki yake mata, can ya girgixa kai yace "No mum, you re misinterpreting me, kar ki ce haka pls, am very different, nasan yanda aka yi na samu Samha don haka i will value her till my last breathe on earth sai dai idan am nt on my right senses" Tace "Toh kuma da ka biye ma sangartattun kannin ka suka ki cin abincinta me hakan ke nufi?" Yyi murmushi yace "You knw it's being long mum, bana son daga xuwansu na fara bata masu rai a kanta it will look somehow, nima i wasn't happy with what they did but it's too early na masu magana, har cikin raina naji hakan da suka yi wllh amma kinga dole bai dace inyi magana a lkcn ba, sai dai kuma i won't take that today" tace "Toh xa mu ga ai" mikewa yyi yace "Mum kenan, kin fi kowa sanin halina fa" tace "Oho nasan ko ka canxa?" Dariya yyi ya nufi kofa yace "Ina nn a yanda kika san ni momma" daga haka ya fita, daki ya shiga yaga bata dakin, ya fita parlor ya ji ta a kitchen, ya karasa kitchen din, Irish take ferayewa ya durkusa kusa da ita yana kallonta yace "Baby da wuri haka, ba bacci nace kiyi ba, how you feeling now?" Ba tare da ta kallesa ba tace "Am fine" yyi shiru yana kallonta, can yace "Kinsa mum na xargin bna kula dake baby whereas it's nt like that, ke ce da halinki at times, sai a rasa gane kanki...." Ganin ko kallonsa bata yi ba ya karbe abun fere dankalin hannunta yace "Ki bari su ilham su xo su yi, mu je kiyi baccin ki" sai a snn ta kallesa tace "A'a xan yi da kai na" ta karbi peeler din ta ci gaba, haka yasa ta gaba yana kallo har ta gama ta mike tana kallonsa shi ma ya mike yace "Sannu da aiki Baby" d'an murmushi tayi bata ce komai ba, sai yaji ddin murmushin da tayi, bude kofar kitchen din aka yi Khaleesat ta shigo, ta langwabar da kai tana kallonsa tace "Good morning bro" yace "Morning kin tashi lfya?" Ta gyada masa kai tace "I want to take cornflakes, is there any?" Yace "Did you greet her?" Tace "Who?" Yace "Ur aunt" kallon mamaki take masa ta sake cewa "Who?" Ya watsa mata wani kallo yace "My wife," turo baki tayi ta juya xata fita ya fixgota yace "Kee! r u stupid ina maki magana xa ki fita?" Ganin bbu wasa idonsa tace "Yaya nayi gaisuwa fa da na shigo" Samha da bata ko kallesu ba tace "She greeted ai" yace "Toh bn ji ba, u greet her immediately now" khaleesat ta d'an kalleta ta wani tsuke baki tace "Good morning" saketa yyi yace "Leave, bbu yara gidan don haka bbu cornflakes" juyawa tayi ta fice daga kitchen din, Samha tace "Sai ka fita ka siyo mata since that's wat she want" yace "Toh ke ki fita ki siyo" tace "Uhm to bani kudin" juyo da ita yyi ya ja hancinta yace "Kiyi amfani da kudin ki idan kina da" daga haka ya lumshe ido yyi kiss dinta kan idon Ilham da ta shigo kitchen din a lkcn, Samha ta turasa ta juya masu baya ta ci gaba da slicing potatoes da take, a takaice ilham tace "Good morning bro, we want custard, is there?" Yace "Kin gaida matata?" Kallon Samha tayi, a takaice tace "Good morning" ba tare da Samha ta juyo ba tace "Ina kwana" Ilham ta dauke kai tace "Lfya lau" ya girgixa kai yace "She's making breakfast now, beside bbu custard gidan nn" juyawa tayi ta fita, ya kalli Samha yace "Baby bari in yi wanka" daga haka ya fita kitchen din, tana soya dankalin aka kwankwasa kofa, ta raga gas din ta fita, khadija ce tsaye bakin kofar, tayi murmushi tace "Sis Samha good morning" murmushin ta mayar mata tace "Morning sis khadija" khadija tace "Dama Ummi ce tace i shud tell you to just make tea nd irish, tana masu girki" Samha tace "Toh shknn" daga haka khadija ta wuce ita kuma ta koma ciki, cikin yan mintuna ta gama ta tsaftace kitchen din ta fito. Dakinta ta nufa ta shiga da sallama ta isa gun Hajiya Mariya ta durkusa tace "Ina kwana mum" Hajiya Mariya tace "Lfya lau my daughter, kin tashi lafiya" tayi murmushi ta gyada mata kai, ta mike tace "Bari in sa maki ruwan wanka mumy" Hajiya Mariya tace "Toh Allah yayi maki albarka" ba a dau lkci ba ta fito tace "Na sa mum" Hajiya Mariya tace "Toh sannu na gode" daga haka ta mike ta shiga bathroom din, gyaran dakin Samha ta shiga yi, ta gyara gadon ta share dakin snn tayi mopping ta kunna turaren wuta ta fita. Daki ta shiga ta samu Abuturrab xaune yana danne dannen laptop, yace "Are you done dear?" Ta gyada masa kai, yace "Toh kin je kin gaida mum?" Tace "Naje" xaunawa tayi d'an nesa da shi ya jawota kusa da shi yace "Sai kyau kike karawa baby" janye jikinta tayi tace "Baxa ka siyo cornflakes din ba?" Bai tanka ta ba ya ci gaba da danna laptop dinsa, wayarsa ce tayi ring ya jawo ya ga Ummi ce ke kiransa, dagawa yyi ya amsa sallamarta snn ya gaisheta ta amsa tace "Boy, clinic nake son kaje may be in d next one hr pls" yace "Toh Mami," tace "Good, ya b'aki?" Yace "Alhmdllh" tace "Toh a gaida min su" yace "In sha Allah" daga haka ya katse wayar, tun da ya dau waya Samha ke kallonsa ko kiftawa bbu, ya ajiye wayar hannunsa ya kalli agogo yaga a lkcn karfe takwas yyi, shafa kansa yyi ya kalleta ganin kallon da take masa da manyan idanuwanta ya hura mata iska, sai a snn ta kifta idon ta dauke kanta da sauri, ya juyo da ita tana facing dinsa yace "Kallon meye wnn kike min baby?" Murmushi tayi ta fara kkrin tashi ya ki saketa yace "No sae kin gaya min ma'anar kallon" dariya take son yi sai dai bata yi ba tace "Ba komai fahh" yace "Ae idan baki fada ba abinda kike pretending baki so ynxun nn xan maki" kmr xata yi kuka tace "Ni fa kawai kallon ka nake" yace "Toh me yasa kike kallona" murmushi tayi ta ki cewa komai, ya xame dankwalin kanta ya kai bakinsa neck dinta, da sauri tace "A'a xan fada...." Ya dago a hankali yace "Toh fada" boye fuskarta tayi a jikinsa murya can kasa tace "Kawai naga kana da kyau ne" ya buda ido yace "Tun da baki san ina da kyau ba sai yau baby" dago kanta tayi tana murmushi, a hankali tace "Yeah, ur eyes, nose, beard, lips.... Everything!" bai ankara ba sai gani yyi ta lumshe ido ta daura warm lips dinta kan nasa and she gave him a deep kiss that made him still. *Haske writers asso* [11/15, 1:47 PM] Fatima gummy: 💫 *Noorul Huda*💫 By Khaleesat Haiydar📚✍🏻 73..... A hankali ta xame jikinta daga nasa xata mike ya rikota da sauri, murya can kasa yace "Noo, finish what you've started baby" bata yrda ta bari sun hada ido ba ta kwace kanta ta dau dankwalinta ta fice daga dakin, lumshe ido yyi yana murmushi, can ya mike xaune yana shafa kansa. Samha na fita parlor ta ga Ilham, khaleesat da fatima a parlon ga cooler din abinci da fatiman ta kawo Ilham har ta xuba waina da miya tana ci, khaleesat kuma na hada tea, bata sake kallonsu ba ta wuce kitchen ta dauko plates da spoon ta fito, ta isa kusa da warmer din abincin ta durkusa ta bude, tun daga sama har kasa fatima ke kallonta, khaleesat ta tabe baki ta dauke kai, Ilham kam ko kallonta dama bata yi ba, Samha ta gama diban wainan ta wuce kitchen ta debi dankali da kwai ta daura a tray hade da wainan ta daura flask din lipton da cup ta dauka ta wuce ta kai ma Hajiya Mariya, fitowa ta sake yi ta dau bread da kayan shayi ta koma dakin ta ajiye, Hajiya Mariya tace "Sannu Samha" murmushi tayi ta juya ta fita, dai dai fitowar Abuturrab rike da laptop dinsa, bata bari sun hada ido ba xata wuce yace "Baby" tsayawa tayi bata dai juyo ba, ya karasa kusa da ita ya tsaya dab da ita yace "Ko mu je clinic din tare ne?" Kallonsa tayi bata ce komai ba, ya gyada mata kai yace "Yea, ko baxa ki ba" ta sunkuyar da kanta tace "Su mum fah?" yace "Ae ba ddewa xa mu yi ba, dauko hijab din ki" tace "Toh baka yi break fast ba" yace "Ohh, alryt just a cup of coffee, sai ki dibar min chips" tace "Ummi ta kawo wainar shinkafa" ya girgixa kai yace "A'a ki kawo abinda nace maki kawai" tace "Toh" snn ta fita parlor, ya koma daki. Har ta shiga kitchen bata kalli inda suke ba, ta gama hada masa abinda yace ta xo ta wucesu, Khaleesat tace "Damn this, wnn arniyar ce xata xo tana daga mana kai a gidan yayanmu" Fatima ta dan bude ido tace "Arniya kuma?" Ilham ta tura cup din gabanta tace "Ehh mana christain" Fatima dake kallonsu da mamaki tace "Ban gane ba" Khaleesat tace "Ohk bai fadi maku Christian ce ita ba knn, she's a nonbeliever, kawai taje tayi tsafinta ta rabamu da yayanmu" kmr xata yi kuka ta kare maganan, Har lkcn kallonsu fatima take kmr bata yrda da abinda suke cewa ba, Khaleesat tace "Ae kafin in bar gidan nn sai na nakada mata duka wllh, kuma sai duk mun gaya ma Mami abinda muka gani" A tare Samha suka yi break din da Abuturrab duk da ta ki da farko, amma yana insisting ta xauna kusa da shi, suna gamawa yasa ta saka Hijab suka fita, sai da suka fara shiga gun small mum dinsa yace mata xa su je su dawo tayi masu Allah ya kiyaye snn ya fito ya dau makullin motarsa a bedroom, kallonsu su ilham suke yi har suka karaso cikin parlor, yyi ma fatima kallo daya ya kauda kai, yana kallon kanninsa yace "You girls shud wash all used plates, kuma ku gyara min dakina ku wanke bathroom" khaleesat tace "Yaya ina xa ka?" Yace "Ba dadewa xan yi ba" Ita dai Samha tana tsaye idonta a kan fingers dinta, Ido fatima ta kafa mata kmr me son gano abinda su ilham suka fadi mata, Khaleesat ta dauke kai tace "Toh shine baxa mu bi ka ba?" Yace "Ae ba yawo xan je ba, gun aiki xan fita, i will be back soon" Daga haka ya kama hannun samha suka nufi kofa, suna fita Khaleesat tace "Damn it, she is d one controlling him" Tun da suka shigo reception ake kallonsu, ya amsa gaisuwar nurses dake gun, Ita ma ta gaishesu duk suka amsa, daga haka ta bi bayansa, duk suka bi ta da ido, wata nurse tace "No wonder his eyes are not on women, his wife is a damsel" yar uwarta ta amsa da cewa "Yea she's beautiful shi yasa yake ma masu crushing dinsa kallon donkeys" wasu daga nurses din ne kawai suka yi dariya, office dinsa ya kai ta ya kunna mata Tv da A.c, ya isa gabanta yace "Enjoy ur self baby, idan kin gaji da xama ki kwanta, i think xamu shiga theatre ne" daga haka ya duka ya manna mata kiss a cheeks dinta yana murmushi ya ja hancinta ya juya ya fita, bai dde da fita ba ta mike ta isa kan bed din duba pregnant women ta kwanta tana kallon movie din da ake a tv, sai kusan karfe sha daya da rabi bacci ya dauketa, bata dde tana baccin ba taji ana shafa fuskarta, a hankali ta bude idonta ta gansa tsaye sanye da surgical clothing, da hula, ya sauke mask din fuskarsa hannunsa daya rike da baby a Shawl, mikewa xaune tayi tana kallon babyn hannunsa ta sauko daga kan bed din da sauri ta wara ido tace "Waow It's a baby!" Dariya ta basa yace "Yea you like babies?" ta gyada masa kai da sauri, mika mata babyn yayi ta rasa ynda xata yi ta karba, har rawa hannunta yake, kallonta yake cike da tausayi tunawa da yyi she's an only child, no siblings, kmr xata yi kuka tace "Ban san yanda xan rike ba doctor" jawota yyi jikinsa ya rungumeta tare da babyn, sai a snn ta iya wrapping babyn da hannunta ita ma tana lekan fuskar jaririn, ya kai bakinsa saitin kunnenta murya can kasa yace "Ke ma kina son ki haifi naki babyn?" Kallonsa tayi ba tare da tayi wani tunani ba tace "Ehh ina so" ya wara ido yace "Da gaske?" Jin ynda yyi maganan ta kuma kallonsa, ganin irin kallon da yake mata ta dauke kanta, ya daura daya hannunsa a flat tummy dinta yana murmushi yace "Soon xa ki haifi naki kema tunda kina so, yau da daddare xa mu samu namu babyn amma mace ni nake so wacce xata yi kama da ke" da sauri ta daga kai ta kallesa dai dai lkcn da aka bude kofar office din doctor Shariff ya shigo, ta sakar masa yaron ta ja gefe, Dr Shariff yace "Ohh ashe tare da madam ku ke Aliyu," Abuturrab yace "Ae kam, Cewa tayi yau sai ta bi ni, ba ynda na iya muka taho tare" yana murmushi ya kare maganan, Dr Shariff yyi dariya yace "Ohh toh sannun ki da xuwa madam, ya gidan?" kanta a kasa ta gaishesa ya amsa da fara'a yana sake welcoming dinta, nan ya dau abinda xae dauka a office din ya fita, Abuturrab ya kwantar da yaron ta karasa tana kallonsa tace "Bacci yake ne?" Yace "Noo he is nt sleeping" xata yi kiss dinsa ya dakatar da ita ya nuna mata lips dinsa yace "Instead ni ki min mana" murmushi tayi ta make kafada, ya ja cheeks dinta yace "i will be right back baby" har ya isa kofa ya juya yace "Kar fa kice xa ki daukesa baby baki iya ba" kallonsa take kmr xata yi kuka, ya danne dariyarsa ya dawo yace "Yes mana baby, idan mun haifi namu sai in koya maki ynda ake daukansu, kina son ki yar masu da jariri ne" yana dariya ya kare maganan, ta fashe da kuka, ya hadiya dariyarsa ya ja ta ya xaunar kan kujera snn ya dawo ya dau babyn ya iso gabanta ya sa mata shi a hannu ta karbesa da murna, yace "Toh kar ki tashi har in dawo" tace "Toh" daga haka ya fita yana murmushi, har ya dawo da wata nurse tana rike da yaron gam sai kallonsa take, da ganinta ka ga sabon shiga, yace "Sannu da aiki wife, kinyi kkri" karban jaririn yyi ya mika ma nurse din ya dau allura da xata yi masa ya bata snn ta fita, kmr xata yi kuka tace "I love babies" xaunawa yyi kusa da ita yace "Toh ba nace yau xamu samu namu ba" mikewa tayi da sauri ya rikota yana dariya yace "Ke fa kika ce kina son babies" tace "Ni na mutane nake so" yace "Uhm? Toh ki fara shirin son naki" Sha biyu suka bar clinic din, ya biya eatery ya siyo take away don bai son tayi wahalan girki ga yan iskan ba ci xa su yi ba, yana gama parking ta bude motar ta fito rike da wasu daga ledojin, shi ma ya fito da sauran, da sallama ta shiga parlon wanda ita ma sai da hakan ya bata mamaki, Suna nn xaune ynda suka bar su, ga plates da cups da suka yi break a gun har lkcn kuma fatima na nn cikinsu, a hankali tace "Sannun ku" bbu wanda ya tanka ta ta wuce ciki, Abuturrab na shigowa ya ajiye ledan hannunsa da mamaki yace "What's all this, kuna nufin tun daxu baku tashi nn ba?" Khaleesat tace "Yaya hira...." Wani tsawan da ya tsorata su ya daka masu, fatima ta tabe baki ta mike ta dau gyalenta ta wuce sa ta fice daga parlon, ya wani daure fuska yace "Before the count of 3 bna son in ga ko wace parasite a nn" mikewa Khaleesat tayi tana murguda baki tace "Toh wai yaya...." Wani ihu ta saki ganin ya yo kanta ta nufi daki gun Small mum dinsu da gudu, Ilham ta bi bayanta har dakin ya bi su, duk suka yi bayan small mum din tasu a tsorace, a fusace yace "Mum wllh xan karya yaran nn a gidan nn idan basu shiga hankalinsu ba, they shud respect their selves idan ba haka ba in yi maganinsu" tabe baki tayi tace "Ni dai kar ku nakasa ni don Allah ku sake ni" yana kallon khaleesat yace "Fita ki kwashe kwanukan nn ki wanke yanxun nn" saukowa tayi daga kan gadon da sauri ta nufi kofan ta fita, yace "Ke kuma tashi ki share gidan gaba daya kiyi mopping, snn ku biyu ku shiga bedroom dina ku gyara ko wani ya kwanan maku a dakin" tashi ilham tayi ita ma tana rabe rabe ta fice da sauri, ya Karasa dakin ya xauna ya gaida Small mum dinsa ta amsa tace "Ina Samhan" xai yi magana sai ga ta ta shigo, ta isa gaban Hajiya Mariya ta durkusa tace "Sannu da gida mum" Hajiya mariya tace "Yauwa Samha har kun dawo" ta gyada mata kai, mikewa Abuturrab yyi ya fita, bedroom dinsa ya shiga yyi wanka ya sauya kayan jikinsa snn ya fito ya wuce daki, Kwance ya ganta yace "Kin gaji ko baby" cikinta ta nuna masa, ya xauna gefenta yace "What happen" a hankali tace "Ciwo yake min" yace "Ciwo kuma?" Ta gyada masa kai yace "Ta ina?" Ta nuna masa gefen cikin, ya sauke ajiyar xuciya yace "Alryt sorry dear, amma ai yana maki hakan koh" ta gyada masa kai, yace "Let me tell you what it is" ya matsa kusa da ita ya duka dai dai kunnenta. *Haske writers asso* [11/15, 8:09 PM] 0mmr Farouk: 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 74.... Bayan la'asar Samha ta fito don daura dinner, yana xaune da su Ilham a parlor gaba daya hankalinsu na kan laptop, ya bi ta da ido har ta shiga kitchen, can ya mike ya bi bayanta, Ilham da Khaleesat suka kalli junansu, a tare suka tabe baki, Ya rungume hannayensa yana kallonta yace "Me xa kiyi baby?" Tace "Abinci xan daura" yace "Ki bar su ilham su yi, since they r doin nothing, beside u re nt feeling fine" tace "A'a xan yi da kai na, am now okay" juyawa yyi ya fita ya koma gun kannin nasa yace "Alryt kallon ya isa haka ku tashi ku shiga ku girka dinner" Khaleesat ta xaro ido tace "Dinner kuma yaya?" Yace "Yes ko breakfast kika ji nace?" Bata ce komai ba ta dauke kai, yace "Ko baxa ku tashi ba?" Ilham ta bata fuska tace "Toh mu ba mu san me xa a dafa ba fa" yace "Ku shiga ku dafa duk abinda kuka ga ya dace" hade rai yyi ganin sun ki tashi yace "You girls shud'nt push me into laying my hands on any of you before leaving this house" ba shiri duk suka mike, ya nufi kitchen suka bi bayansa khaleesat har da hawayenta, yana shiga kitchen din ya janyo Samha suka fita, kallon mamaki take masa tace "Meye haka doctor?" Yace "Nace baxa ki yi girkin ba nurse" daga haka ya ja ta ya komar da ita daki. Tagumi Rachael tayi tana kallon priest din dake xaune gabanta, Vivian dai sai gyara gyaran zama take don ta gaji da xaman, sun fi awa daya zaune gaban priest din har lkcn bai ce komai ba, priest din ya d'ago kai daga karshe ya nisa yace "Rachael!" Mahaifiyar Samha ta gyara xama da sauri tace "Na'am Father" ya girgixa kai yace " 'yar ki xata dawo, sai dai ba ita kadai ba" Rachael na kikkifta ido tace "Tohhh... Ita da wa Father" yace "ita da jikokin ki" kallon Sarah tayi a rikice tace "God forbid!" Nan da nn idonta ya kawo ruwa cikin raunin murya tace "Jikoki kuma Father??" Yace "Kwarai kuwa" ta fashe da kuka sosai tace "Blood of jesus, Ai ni nasan na shiga uku na lalace, amma yaushe kaga dawowan nata father?" Yace "Wannan kuma sai mu bar ma Jehovah sani" Ta kuma rushewa da kuka tace "Father ya xan yi da raina, wnn 'ya ita knn gare ni, ni kadai nasan abinda nake ji rashin Rebecca, nayi kwanciyar asibiti ya fi a kirga, to 'ya yan ubanwa xata taho min da..." Ta kuma rusa wani uban kukan tace "Amma Jehovah ya isa tsakanina da musulmin nn, ya cuce ni ya cuceni" Vivian dai tagumi kawai tayi bata ce komai ba, Priest din ya girgixa kai yace "Am giving u assurance yarinyar ki xata dawo gare ki sai dai xa a dau lkci me tsawo kuma Allah bai nuna min lkcn ba, sai dai ina son ki sani cewa akwai sa hannun yan uwan mijin ki a lamarin nn, wasun su kuma sun san inda take" Rachael ta share hawayenta da sauri tana xaro ido tace "yan uwan mijina kuma father?" Ya gyada mata kai yace "Kwarai kuwa" Tace "Heyyy! father yan uwansa uku ne ke raye ae yanxu.... Daga Sarah sai wata Maryam dake kaduna sai yayarsu dake Ghana to waye cikinsu xae cuce ni haka, nasan Sarah baxata cuceni ba" sai ta kuma fashewa da wani sabon kukan tace "Sae dai algungumar musulman nn Maryam, kai ni na ma san ita ce, amma Allah ya isar mani tun a duniya" Sarah tace "Ki kwantar da hankalin ki sister, in har Maryam ce sai tayi regretting action dinta, ni dama tun da naji musulma ce matar nn kwata kwata ta fice min a rai, in har tasan whereabout din Samantha ta bari muke ta garari sai na yi mata abinda har ta bar duniya baxa ta mance ba" Rachael na share hawayen fuskarta tace "Man of God wani aiki nake son ka min don Allah" ya gyada kai yace "Fadi me kike so" ta kara gyara xama ta tsuke fuska a nutse tace "So nake ka min addu'a wanda xai sa Samantha tayi da ta sanin bin musulmi, so nake kasa shi musulmin ya mayar da rayuwarta so miserable, so nake kasa ya walakantata karshen wlknci infact he shud just make life worst nd miserable for her" tana huci ta kare maganan, Priest din na jinjina kai yace "Wnn abu me sauki ne ai" Tace "Sai dai fa kar ayi wanda xai sa in rasa 'ya ta, kawai dai a d'an wujijjigata ne ta dawo gida, snn wnn jikan da kace xa a taho min da kayi duk abinda xaka yi kar ya iso duniya" Daga haka ta bude jakarta ta fiddo kudi me yawa ta ajiye masa tana godiya, Vivian tace "Toh shi dan iskan a haka za a bar shi?" Rachael tayi murmushin mugunta tace "Jira 'ya ta ta dawo gare ni ki ga abinda shi kuma xan masa" daga haka ta mike tsaye suka sallami priest din suka fita. Da daddare Abuturrab na xaune tare da Small mum dinsa a daki tace "Gobe fa xa mu koma Haiydar" ya kalleta yace "Gobe kuma mum?" Tace "In sha Allah" ya marairace mata yace "But i thought sati xa ku yi ae" ta hararesa tace "So kke col ya dau hanyar yobe don dauko yaransa koh?" Murmushi yyi yace "Toh mum su koma su sai ke kiyi sati daya" ta kuma hararansa tace "Aikin sai in bar maka knn" ya bata fuska yace "Mum to sai yaushe kuma?" Tace "Ranan da kaje kano" murmushi ya kuma yi bai ce komai ba, can yace "toh amma da yamma xa ku tafi ko mum?" Tace "Sai mu isa da yaushe?" Yace "Sai in biya maku flight mum" tace "Noo, da safe xa mu wuce Aliyu, kar ka damu xan dawo wani lkcn" bai kuma cewa komai ba, sae dai yaji har ya fara missing din mum din tasa da sisters dinsa, sun jima suna hira daga bisanni yyi mata sai da safe kusan karfe sha biyu, bedroom dinsa ya bude ya ga sisters dinsa har sun yi bacci ya rufe masu kofa ya wuce daki, ita ma Samha har tayi bacci, ya kashe wutan dakin ya kunna Ac ya cire jallabiyan jikinsa ya isa kan gadon ya xauna gefenta yana shafa fuskarta, a hankali ta bude ido ya duka dab da ita yace "Haka muka yi da ke?" Kmr xata yi kuka tace "Doctor bacci naki ji" kwanciya yyi gefenta yace "Toh yi baccin ki wife" juya masa baya tayi ya jawota jikinsa a hankali. Da asuba yana dawowa masallaci ya tarar har ta tashi ya xauna gefen gado yace "Baby yau fa su mum xa su wuce" tace "Yau kuma" ya gyada mata kai, ta langwabar da kai tace "So early?" Mikewa yyi yace "Yea, just a day leave ta dauka a gun aiki" karfe tara mum ta gama shiryawa bayan sun yi breakfast, su ilham ma duk sun gama shiryawa, Samha ta bi Abuturrab bedroom tace "Doctor ni bn san me xan ba su ilham ba" ya juya ya kalleta, sai kuma yyi murmushi yace "don't worry i will give them on ur behalf baby, laifina ne bana baki kudi koh?" Tace "Toh idan ka ban kudi me xan yi da shi?" Yace "Ga irin abinda xa kiyi da shi nn ai" bata ce komai ba ya ja hancinta yana murmushi yace "Toh mu je mu kai su park" ko da suka fito parlor khaleesat ce kadai tana sa jewelries dinta, yace "Ina mum?" Tace "Ta je part din su fatima" yace "Ohk" bayan kusan minti sha biyar Ummi suka taho tare da Hajiya Mariya, sai kusan karfe goma suka bar gidan bayan ta ba Samha turarruka masu yawa da ta hado mata har da na wuta, ta kuma yi mata nasiha sosai ta bata shawarwari, suna isa park Hajiya Mariya tace "Aliyu kayan ka na booth na mance ban fada maka ba wllh" yace "Toh mum" shi ya biya masu kudin mota duk da ynda Hajiya Mariya ta dinga hanasa, ya ba kanninsa dubu goma bayan sun karba yace "Samha tace a baku" kallonta suka yi gaba daya, khaleesat ta dauke kai hade da kyabe baki, Hajiya Mariya ta ja Samha ta bude jakarta ta ciro box din dankunne ta mika mata tace "Gashi daughter ki sa a kunnen ki, sae na dawo wani lkcn kin ji" sunkuyar da kai Samha tayi lkci daya hawaye ya cika idonta ta dan risina ta karba cikin sanyin murya tace "Nagode mum" Hajiya Mariya tayi murmushi ta dago kanta tace "Kuka kuma Samha" girgixa mata kai Samha tayi tana kkrin mayar da hawayen, Abuturrab dake tsaye tare da su Ilham ya juya ya kallesu yyi murmushi ya dauke kai, Khaleesat da har ta fara hawaye tace "Yayanmu yaushe xaka dawo gida plss" Ya kama hannunta yace "Soon sweet sis, ku gaida min da Ramla sosai kuce mata i missed her a lot" Ilham ta fashe da kuka ya wara ido yace "Kee a park din kuma" jawota yyi ya rungumeta yace "Kar ku damu sisters, soon xan dawo gida kun ji" A haka mota ta cika Hajiya Mariya ta fara shiga snn Khaleesat dake hawaye, yana rike da hannun Ilham ta shiga motar don kin sakesa tayi, yyi pecking hannun nata yace "I will miss you all sisters" daga haka ya xame hannunsa, sai kallonsu mutanen cikin motar suke, Ya daga ma Small mum dinsa hannu snn ya juya ya bar gun, banda kuka bbu abinda Samha ma take, motar na fara tafiya ta daga ma su Ilham hannu, Yayansu suka kalla kafin su daga mata hannun su ma, murmushi yyi ya bi motar da ido har suka fita park din kafin ya juya ya bude front seat yana kallon Samha yace "Toh kukan ya isa haka shiga mu tafi" tana shiga motar ya rufe ya xaga ya shiga maxaunin driver. Sai sha daya suka isa gida yana gama parking ya bude booth snn ya fito ita ma ta fito, ya xaga ya bude bayan booth din yana kallon jakar kayan dake ciki da cooler ya dau coolern ya mika mata, snn ya fiddo jakar ya rufe booth din yana kallonta yace "Still crying?" Dauke kanta tayi, yayi murmushi yace "Toh mu je ciki in lallashe ki" gaba tayi ta bar sa a gun, tana shiga parlor ta ajiye coolern hannunta ta wuce daki ta fada kan gado ta ci gaba da kukanta, a dakinsa ya ajiye jakar snn ya shiga inda take ya kwanta gefenta ya jinginar da kansa da nata yace "So dai kike in lallashe ki ko baby, ohk then" mikewa xaune yayi ya dagota ya fara kissing dinta, tun tana son kwace kanta har ta gaji ta hakura, ae ko ya lallasheta yanda ya kamata, sai kuma ta 6uge da kukan shagwaba daga shagwaban kuma sai bacci, jin xa'a tada sllhn zhur yasa shi mikewa don har ya fara bacci shi ma, ya shiga bathroom yyi wanka ya dauro alwala ya fito, ya gabatar da sllhn a daki don har an idar masallaci, bayan ya idar ya koma yyi kwanciyarsa. Sai kusan karfe uku Samha ta farka ta kalli agogo snn ta kallesa, a hankali ta kai hannu fuskarsa, ya bude ido a hankali tace "You've nt prayed zhur" jawota yyi jikinsa ya lumshe ido yace "Nayi mana baby, amma kinsa nayi missing jam'i" ta buda ido tace "Ni kuma" yace "Ehh mana, u made me left this world" rufa fuskarta tayi a kirjinsa, yyi murmushi yana shafa dogon gashinta, can ta xame jikinta yaki saketa yace "Ina xa ki?" Tace "Wanka" saketa yyi yace "Toh muje in maki" Wani kallo tayi masa ta fice daga dakin da sauri, dariya yyi yace "What is she still hiding?" *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By Khaleesat Haiydar📚✍🏻 75..... Da daddare suna bedroom ta dauko box din da Hajiya Mariya ta bata ta mika masa tace "Mum ta bani wnn" karba yyi ya bude ya wara ido yace "Ehen, nine knn ba a ba komai ba, a gold for you!" Tayi murmushi tace "Kaga ta fi so na" ya langwabar da kai yace "Gashi nn naga alama" daukan dankunne daya yyi ya cire mata na kunnenta ya sa mata, ya cire dayan ma yasa yace "Uhmm you're glittering" lumshe ido tayi, yyi pecking dinta yace "I love you wife" a hankali ta kwanta jikinsa cikin sanyin murya tace "I love you more" 3wks ltr. Abuturrab na bedroom misalin karfe tara da rabi, fitowarsa daga wanka knn yana shiryawa da yake saturday ne sai yamma yake fita gun aiki, k'auri ya dinga ji ya juya yana kalle kalle sai kuma ya ajiye hair brush din hannunsa ya fita da sauri, yana shiga kitchen din ya ganta xaune kasa ta jingina da bango tana bacci, ya kalli irish din dake cikin mai har ya fara baki ya kashe gas din, durkusawa yyi gabanta yana kallonta, can ya kamo hannunta ya sauke idanuwansa kansu, a hankali ta bude idonta, ya tsura ma idanunta ido, murya can kasa tace "Doctor.... Am feeling sleepy" Murmushin da ya bayyana fararen hakoransa yyi yace "Koh?" Kmr warce ta tuno abu ta wara ido ta mike tsaye da sauri tana kallon pan din dake kan gas, kallonsa tayi kmr xata yi kuka tace "Doctor ya kone, i don't knw...." Rufe bakinta yyi ya ja ta suka fita daga kitchen din ya kaita daki ya xaunar da ita gefen gado, ya kanne mata ido yace "Ke fa kika hanani bacci daren jiya da shagwaban ki baby, ni ban yi bacci a bathroom ba da naje wanka sai kece xaki je kitchen kina bacci ki kona mana abinci?" Kallonsa take kamar xata yi kuka, yayi dariya ya shafa fuskarta a hankali yace "Toh yi hakuri wife, bari in shirya sai in fita in siyo mana breakfast, go nd take ur bath" turo baki tayi ta mike ta nufi bathroom ya bi ta da kallo yana murmushi, har ya gama shiryawa ya fita nearest fast food ya siyo abinda xae siyo ya dawo bata fito daga wanka ba, mamaki ne ya cika sa, ya ajiye ledojin hannunsa ya bude kofar bathroom din, kwance ya ganta cikin bathtub ta tara ruwa tana ta bacci ciki abunta, xaro ido yyi ya karasa wajen ya durkusa ya kashe ruwan yana kallonta murya can kasa yace "Toh fah" hancinta ya ja ta bude ido da sauri yace "Nan din ma baccin kika xo kina yi baby?" Kalle kalle ta fara yi, ya girgixa kai ya jawo sponge tana nonnokewa har ya gama ya fito da ita daki, gaba yasa ta har ta gama shiryawa kar ta kuma yin baccin, yana kallon lumsassun idonta yace "Har ynxu baccin kike ji koh?" Kai ta gyada masa yace "Toh bari kiyi breakfast sai ki kwanta" ta girgixa kai tace "Bana jin yunwa ynxu" shiru yyi yana kallonta, can yace "Alryt kwanta baby" kwanciya tayi kan gadon yyi murmushi ya mike ya fita don hado coffee, ko kafin ya dawo har tayi bacci, haka ya xauna kusa da ita ya tsura mata ido yana kallo, wani kyau na musamman yaga ta kara da haske, can underneath his breathe yace "Waow!" Juyawa yyi jin ringing din wayarsa ya mike ya isa gaban mirror ya dauka ya ga Ummi ce ke kiransa, ya langwabar da kai yace "Oops" bai yi budgeting fita da safe yau ba, a hankali ya daga wayar ya kai kunnensa ya amsa sallamarta snn ya gaisheta, tace "Kun tashi lfya boy?" Yace "Alhmdllh Mami" tace "To Madallah, hope baxan takura ka ba boy xan sa ka aiki coz m nt around...." Yace "Not at all Mami" tace "Alryt, fatima nake son ka dauko daga makaranta, Asthman ta ne ya tashi, xan baka number kawarta ku dinga communicate har ka je can...." Yace "Subhanallah, suna lectures weekend ne?" Tace "Not at all, ae tafi sati biyu a schl, a hostel take" yace "Alryt mami, buh is she with her inhaler?" Tace "They can't find it, daga can kawai ka wuce clinic da ita ko allura ne ayi mata" yace "Toh Mami bari in tafi ynxu" daga haka ya katse wayar ya mike yana kallon Samha, lullubeta yyi da bargo, ya kashe Acn dakin ya sake mata curtains, ya daura lips dinsa kan forehead dinta yace "I wil be right back wife" daga haka ya dau makullin mota da wayarsa ya fita, yana warming motar message ya shigo wayar yaga Ummi ce ta turo masa number kawar fatima Salima, sai da ya bar compound snn ya kira number, ba a jima yana ringing ba aka dauka yyi sallama, daga daya bangaren aka amsa, yace "Salima ce?" Tace "Yea..." Yace "Ya jikin fatiman?" Tace "To ga ta nan dai" yace "Kuna hostel din ne?" Tace "Ehh wai da clinic xamu wuce ynxu it's getting worst" yace "Noo kar ku je ina hanya ynxu" daga haka ya katse wayar, yana isa makarantar ya kuma kiranta tayi masa kwatancen inda hostel din nasu yake, ya jira su har suka fito su uku da Fatiman, Fitowa yyi ya bude back seat yana kallonta yace "Sorry," sai da ta shiga motar snn ya kalli frnds dinta yace "Thanks much, xa mu tafi hospital da ita ynxu" Salima tace "Toh ba sai mun bi ku ba knn" yace "Noo kawai ku koma ciki nasan kila ma karatu ku ke" daga haka yyi masu sallama ya xaga ya bude driver seat ya shiga duk suka bi sa da ido, ya rufe motar ya tada ya dau hanyar gate, ta madubi yake kallonta jefi jefi, sai yaji tausayinta ganin tana jin jiki, yace "Fatima" da kyar ta dago don dama kife kanta tayi, yace "You sit upright, kar ki sake dukawa" mayar da kanta tayi, bai kuma cewa komai ba ya d'an kara speed, suna isa clinic, yyi parking ya fito ya xaga ya bude mata motar ya dagota, hijab din jikinta ya cire ganin rigar dake jikinta ya d'an kamata, ya kai hannu bayanta ya d'an bude zip din ya mayar mata da hijab dinta ya fito da ita daga motar suka shiga asibitin, dai dai sakkowar Dr Shariff daga sama, yana ganinsu ya nufo su yace "Subhanallah" Nurses biyu dake wajen su ma suka yo kansu suna mata sannu, Abuturrab ya mika masu ita yace ku shiga da ita wancan ward din Shariff ya bi bayansu, Pharmacy Abuturrab ya shiga ya karbi alluran da xai mata snn ya fito ya wuce ward din, har Dr Shariff ya cire mata hijab din jikinta ya xaunar da ita ta jingina da bango kan gadon, shi dai Abuturrab kallonsa kawai yake ganin ynda ya wani daga hankali, kawai ya mika masa alluran yace "Gashi kayi mata" Dr Shariff yace "Inhaler dinta fa wai" Abuturrab ya bude hannu alamar bai sani ba, daga haka ya juya ya fita don basa waje yyi mata alluran, ba a dau lkci ba Shariff ya fito yana kallon Abuturrab yace "Let me get her another a office din Dr" daga haka ya wuce sama xuwa office din Ummi, murmushi Abuturrab yyi, bayan yan mintuna sai ga shi ya sakko da sabon inhaler ya shiga ward din, Abuturrab ya bi sa yace "Tunda kayi mata injection kawai ka bar inhaler din, she will be fine soon" Dr shariff yace "Ohh, exactly" murmushi Abuturrab yyi ya juya ya fita, ba a dau lkci ba bacci ya dauke fatima bayan numfashinta ya fara yin dai dai sai a snn Shariff ya fito, shi dai Abuturrab na xaune duk hankalinsa yyi kan Samha, ya mike yana kallon Shariff yace "In tafi kawai xaka mayar da ita gida Dr?" Shariff yace "Am attending to patient ae, sae dai idan xaka tsaya sai in mayar da ita gida,n" Abuturrab yyi dariya yace "Nima matata na can gida na baro ta ba lfya" Shariff yace "Alryt then, ka jira ka mayar da ita kawai" Sai bayan kusan minti talatin fatima ta dawo dai dai, Abuturrab dai na ta xaune duk hankalinsa na kan wife dinsa, karfe sha daya ta fito daga ward din, Abuturrab ya kalleta ya mike yace "How you feeling now" ba tare da ta kallesa ba murya can ciki tace "Fyn" bai kara minti biyar clinic din ba suka wuce gida tare. Yana gama parking ta bude motar ta fita gabansa ya dinga faduwa kar Samha ta ganta ya shiga uku, sai da yaga tayi nisa ta kusa part dinsu snn ya fito daga motar, sae a snn ya tuna ko godiya bata yi masa ba, ya bi ta da wani irin kallo, dai dai lkcn da ta juyo ta kallesa suka hada ido, murmushi yaga tayi ta yi gaba abun ta, ya d'an yi tsaki ya wuce ciki, ga mamakinsa har lkcn bacci Samha take, ya xauna gefenta ya langwabar da kai yace "Wnn wani irin baby ne xai dinga sa min wife dita bacci haka" ji yyi kmr ya tasheta tunawa da yyi bata karya ba har lkcn, ya dai kyaleta kawai ya mike, ana kiran sllhn zuhr ya tasheta, ya kai ta bathroom ta wanke bakinta ya wanke mata fuska ya fito da ita sai layi take masa, da kansa ya dinga bata tea din da ya hada mata, ta sha me yawa kafin tace ta koshi, xata kwanta yace "Baby baccin ya isa haka plss, mu je in kai ki yawo ki ga gari" kmr xata yi kuka tace "Kawai kwanciya xanyi baxan yi bacci ba" xai yi magana wayarsa ya fara ring yana ganin Ummi ce ta langwabar da kai, can dai ya daga tace "Boy sannu da kkri fa, Allah yyi albarka" yace "Amin Mami" tace "Ka turo min Samha ynxu" ya kalli Samha da ta kwanta ta lumshe ido, yace "Toh Mami" yana katse wayar ya dagota yace "Baxa fa ki kara wani baccin ba" kwace kanta tayi a fusace tace "Did i tell you am sleeping??" sai da ya runtse ido jin tsawan da ta daka masa, can ya bude idon a hankali yace "Ohk am sorry wife, dama Mami ce tace ki je" ta kallesa da sauri tace "In je?" Yace "Yes she just called" a hankali tace "Amma sai anjima koh? I dnt feel like going out" Yace "Noo, ki je ynxu baby kilan jira take" da kansa ya dauko mata hijab ya mika mata ta karba ta sa, ta mike ya rakata har balcony, a hankali tayi sallama ta bude kofar parlon ta shiga, ji tayi kanta na juya mata kamshin miyan da ake a kitchen, ta karasa ta xauna da kyar tana kallon Ummi ta gaisheta, Ummi dake ta kallonta tace "Bacci kike ne daughter" a hankali tace "Na tashi Ummi" Ummi dai sai kallon kwayar idonta take, can tace "Alryt, ki gaya min ko da abinda kike bukata, i mean anything... " Samha ta kalleta, can tace "Ba abinda nake bukata Ummi" Ummi tace "A'a kar fa ki ji komai beside hakkin ki ne, sadakin ki ne...." Ta girgixa kai kawai jin cikinta na hautsinewa, cike da karfin hali tace "Ba komai Ummi" Ummi da ta lura da yanayinta tace "Are you okay?" Mikewa tayi da sauri tana toshe baki, Ummi ta mike ta kamota ta nufi toilet dake parlon da ita da sauri, kafin ta shiga ta fara kwarara aman a wajen, Ummi na tsaye sai sannu take mata, can ta duka ta riketa ganin ta galabaita, sai da aman ya tsaya mata snn ta dagata suka shiga bayin, ta taimaka mata ta wanke bakinta, ta cire hijab din jikinta ta ajiye cikin bucket dake bayin, jin temperature dinta ya d'an yi sama ta xuba mata ruwa kadan a kanta snn ta ja ta suka fita daga bayin, Samha ta toshe bakinta hade da hancinta don ko da wasa bata son ta kara jin aroman miyan, hakan yasa Ummi ta fitar da ita gaba daya daga gidan, tana rike da ita ganin duk tayi weak ta wuce part dinsu da ita. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 76..... Yana xaune parlor ya bude laptop knn Ummi tayi sallama suka shigo parlorn, mikewa yyi ya amsa sallaman, Ummi ta xaunar da ita kan kujera tana mata sannu, bata iya ta amsa ba ta kwanta tana mayar da numfashi, Ummi ta kallesa tace "Wani taimakon ka bata?" Ya d'an sosa kai ba tare da ya kalleta ba yace "Mami... nothing yet" tace "To sbda me?" Still bai kalleta ba yace "I just saw the symptoms this morning Mami" Mami na kallonsa tace "Toh yyi, Allah ya kawo mata da sauki, naga bata ci komai ba sai ruwan shayi" yace "She have being sleeping tun da safe, sae da na dawo clinic daxu ma na bata shayin" Ummi ta kalleta ta xauna gefenta tace "Me kike son ci daughter" a hankali ta bude ido tace "Bana jin yunwa Ummi" Ummi tace "A'a you've nt taken anything today, ko a kawo maki shinkafa...." Da sauri tace "A'a..." Ummi tace "Toh me kike so" shiru tayi, sai kuma a hankali tace "Kila tuwo xan ci" Ummi tace "Tuwo?" Ta gyada kai, Ummi tace "Da wani miyar?" Tace "Miyar ganye" mikewa Ummi tayi tace "Toh bari a maki" daga haka ta fita, Abuturrab ya xauna gefenta yana shafa fuskarta yace "Amai kika yi baby?" Kmr xata yi kuka tace "Bana son kamshin miyan" ya lumshe ido ya bude a hankali yace "Sorry babyna, in'sha Allah baxa mu yi wahala sosai ba" ta kallesa tace "Na mene?" Murmushi yayi ya hade goshinsa da nata, murya can kasa yace "Komai ma" Kauda kanta tayi, ya juyo da fuskarta yace "Baxa ki ce Amin ba wife" kallonsa kawai take don ko magana ma bata son yi, can ta lumshe idanuwanta, yyi murmushi ya koma kan laptop dinsa. Bayan awa daya Usaina ta shigo parlon da sallama ta gaida Abuturrab snn ta ajiye abincin hannunta ta fita, mikewa yyi ya nufi kitchen ya dauko plate da spoon ya isa inda Samha take tana bacci ya xauna gefenta ya daura hannu fuskarta yace "Baby ga tuwon an kawo maki, tashi ki ci...." A hankali ta bude idanuwanta ya daga ta ta xauna snn ya sauka kasa ya bude warmer din tuwon ya dibar mata ya rufe, kallonta yyi yaga ta jinginar da kanta da kujera ta rufe idonta, ya bude miyan ya dibar mata a kan tuwon da nama snn ya tashi ya xauna kusa da ita yace "Gashi baby" a hankali ta bude idanuwanta, lkci daya ta kauda kai da sauri ta matsa daga gun tana girgixa masa kai tace "Zan yi amai" yace "Miyan da kika ce kina so ne ae dear" taki juyowa sai girgixa masa kai take, ya mike ya dawo kusa da ita tana ido hudu da abincin ta fara yunkurin amai, mikewa yyi ya koma baya, ta fashe da kuka tace "Bana son in ga abincin doctor amai xan yi" daga haka ta tashi ta wuce daki da sauri, ya bi ta da kallo, can ya sauke ajiyar xuciya ya ajiye abincin ya xauna gefen kujera, mikewa yyi ya bi bayanta, durkushe ya ganta cikin bayi ya isa kusa da ita, tana kallonsa da kyar tace "I want to throw up doctor, ya ki xuwa" durkusawa yyi kusa da ita yace "It's because u haven't taken anything wife" ta girgixa kai tace "Baxan iya ba" dagota yyi suka fita daga bayin ya xaunar da ita gefen gado yace "Toh in kawo maki tea xa ki sha?" Kai ta gyada masa ya kwantar da ita yace "Toh ina xuwa" daga haka ya fita ba a dau lkci ba ya dawo rike da cup din tea, ba laifi ta sha tea din kmr daxu snn ta koma ta kwanta. Tun daga wannan rana Samha tayi bankwana da lafiya, laulayi take me tsanin wanda hakan yasa ya dinga tausayinta ba kadan ba ganin shekarunta, d'an ruwan tea'n da ta ke sha da farko farko shi ma yanxu idan ta sha sai ta amayar gaba daya, bbu abinda take iya ci sai gayan shinkafa shi ma sai an ci sa'a, hakan yasa Ummi ke yi mata kunu shi ma bai fi ta sha sau daya a rana ba, duk ta rame ba kadan ba sai haske, shi kansa ya rame sai ka rantse tare suke ciwon, ko kadan bai son wnn laulayin da take, wani lkcn sai yaji xuciyarsa na urging dinsa kan ya rabata da cikin don wahalan yyi yawa, sosai Ummi ta d'aga masa kafa kan xuwa gun aiki don sai yyi kwana uku bai fita ba, Duk yamma khadija kan shigo tayi share share tayi mopping ta kuma wanke plates idan akwai used ones a kitchen, har bedroom wani lkcn ta kan gyara ta wanke bathroom, lkci lkci kuma Ummi ta kan shigo duba Samha, ita kanta bata jin ddin ynda taga tana wahala sosai, kmr ko da yaushe yau ma da daddare Ummi ta shigo har bedroom don dubata, can dai ta kalli Abuturrab tace "Anya kana kara mata ruwa tana kuma shan drugs boy, she look so sick?" Yace "Ina dai sa mata ruwan, amma bata yrda ta sha maganin Mami, bn san ynda xan mata ba, alluran ma bata so" Ummi ta kalleta tace "Ki daure ki dinga shan drugs kin ji daughter, hakan xae sa ki dinga jin kwari a jikin ki, ko ba ki son ki samu lfya da wuri?" Samha ta girgixa mata kai kawai, Ummi ta d'an jima dakin kafin ta wuce bayan ta tilastata ta sha kunu ta kuma sha magani, ae ko minti goma Ummi bata yi da tafiya ba duk ta amayo su, kallonta kawai ya tsaya yana yi, can ya mike ya isa kofar bayin ya durkusa a hankali yace "Yanxu wife sai da kika yi aman d'an kunun nan" bata ce masa komai ba kanta a kasa, ya mike ya shiga bayin ya hada mata ruwan wanka, ya taimaka mata tayi snn ya wanke gun aman, duk da uban bargon da ya rufa mata hakan bai hanata rawan sanyi ba, ya dauko wani bargon ya kuma rufa mata ya xauna gefenta yana kallonta, sai da yaga alamar ta fara bacci snn ya mike ya fiddo mata doguwar riga ya dawo ya cire bargon, a hankali ta bude ido tana kallonsa, ya dagota ya sa mata rigar ya rungumeta yana shafa gashin kanta murya can kasa yace "Sorry wife, soon xa ki samu lfya kin ji" a hankali yaji tace "Ina son in kira Abbana" shiru yyi abinda ta fada na d'ad'a sinking a kansa, can yyi karfin halin cewa "Abban ki??" Kai ta gyada masa ya rasa abun ce mata, suna nn a haka har bayan minti kusan goma yaji saukan numfashinta a hankali, lumshe ido yyi ya bude, ya kwantar da ita yana kallonta. Washegari da misalin goma ya tafi part din Ummi, ya ci sa'an samunta a balcony tana waya, ya xauna ya jira har ta gama sannan ya gaisheta ta amsa tace "Ya mai jikin?" Yana shafa kai yace "Alhmdllh, Mami dama...." Sai kuma yyi shiru, tace "Ya aka yi boy?" Ya kuma shafa kansa yace "Mami i think she's too young to conceive, shi yasa take wahala haka, it's just two month and..." Sai kuma yyi shiru, ta ajiye wayar hannunta tace "Yea she's young, So what's ur opinion in here?" Kallonta yyi a hankali yace "Mami kawai a cire mata, may be some other time...." Ummi na masa wani kallo tace "Really?" Sunkuyar da kai yyi bai ce komai ba, can tace "Never knew u where this stupiddd sai ynxu, to tun da kai kayi halittan dake cikin nata sai ka je ka kashe sa ai, pls get out now" bai iya ya dago kansa ba ya kuma kasa tashi, tace "Bani waje nace Aliyu" da kyar ya bude baki yace "Am sorry Mami, am just confused, bn san wani tunanin xan yi ba kuma..." Tace "In dai ka taba halittan ko da kwaro ne to kaje kayi abinda xuciyar ka ke raya ma" mikewa yyi har lkcn bai dago ba yace "Kiyi hakuri Mami" tace "Foolishness dinka dai xaka ba hakuri" murmushin karfin hali yyi ya juya ya bar gun, ko da ya koma a bathroom ya sameta a durkushe, ya tsaya bakin kofar ya rungume hannayensa yana kallonta, ta juyo da kyar ta kallesa, shiga bayin yyi ya karbi brush din hannunta ya ajiye, kullum da shi take tono ma kanta aman safe, in dai xata yi to sai tayi amai, ya debi ruwa ya xuba gun aman snn ya kama hannunta suka fita, ta kwanta tana mayar da numfashi a hankali tace "Ina son xan yi magana da Abbana" *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By Khaleesat Haiydar📚✍🏻 77..... Jin bai ce komai ba ta juyo tana kallonsa, d'an murmushi yyi yace "Baby me xaki ce ma Abba" ta kauda kanta murya can kasa tace "I just want to talk to him" shiru ya kuma yi har sai da ta sake juyowa snn yace "Yanxu?" Ta gyada masa kai, yace "Do you have the number" nan ma gyada masa kai tayi, ya mike duk jikinsa yyi sanyi ya dauko waya ya dawo kusa da ita yana kallonta yace "Fadi number to?" Hannu ta buda masa alamar ya bata wayar, ya sa mata a hannu ta saka number snn ta kallesa, karban wayar yyi, yyi sending number snn ya kai kunne, haka kawai gabansa ke faduwa, sai da ya kusa katsewa aka daga wayar, muryar Abbanta ya daki dodon kunnensa, Mr David yace Hello yyi sau uku, Abuturrab ya kallesat snn ya mika mata wayar ta karba ta daura kunnenta, mikewa xaune tayi jin muryar Abbanta a hankali tace "Abba" Jin bai ce komai ba ta juyo tana kallonsa, d'an murmushi yyi yace "Baby me xaki ce ma Abba" ta kauda kanta murya can kasa tace "I just want to talk to him" shiru ya kuma yi har sai da ta sake juyowa snn yace "Yanxu?" Ta gyada masa kai, yace "Do you have the number" nan ma gyada masa kai tayi, ya mike duk jikinsa yyi sanyi ya dauko waya ya dawo kusa da ita yana kallonta yace "Fadi number to?" Hannu ta buda masa alamar ya bata wayar, ya sa mata a hannu ta saka number snn ta kallesa, karban wayar yyi, yyi sending number snn ya kai kunne, haka kawai gabansa ke faduwa, sai da ya kusa katsewa aka daga wayar, muryar Abbanta ya daki dodon kunnensa, Mr David yace Hello yyi sau uku, Abuturrab ya kalleta snn ya mika mata wayar ta karba ta daura kunnenta, mikewa xaune tayi jin muryar Abbanta, lkci daya taji wani farin ciki har cikin ranta, a hankali tace "Abba" Mr David dake bedroom dinsa ya mike xaune daga kwancen da yake yana son tabbatar da muryar da yake ji, cikin rawar murya Samha ta kuma cewa "Abba...." Ya mike tsaye da wani irin mamaki yace "Daughter?" Hawaye ne ya sakko idonta cikin sanyin murya tace "Good morning Abbana" Ya koma ya xauna yace "Samantha?" Ta fashe da kuka tace "Abbana" bai iya ya kuma ce mata komai ba, tace "Abbana kayi hakuri...." Ya girgixa kai yace "Where are you Samantha" kallon Abuturrab tayi ta kasa cewa komai, Mr David yace "No, you talk to me daughter kina ina, where r u please" hawaye kawai ke sakko mata ta sunkuyar da kai tace "Ina nan Abba" yace "kina ina? Tell me Samantha" Ta kuma kallon Abuturrab da ya kasa kallonta, kashe wayar tayi ta kife kanta ta dinga rera kuka, wayar ya fara ring har ya katse bata daga ba, shi dai Abuturrab bai ce komai ba, Sau uku Abban nata ya kira taki dagowa bare tayi picking call din, a na hudun ne Abuturrab ya karbi wayar ya daga a hankali ya kai kunnensa, Muryar mahaifin nata yaji yana cewa "Don't cut the call again pls daughter, i am talking to you ki saurare ni don Allah" Abuturrab yaji tausayinsa jin yanayin muryarsa, da kyar yyi gathering courage ya lumshe ido yace "We re sorry for everything dad, i knw i did wrong but.... God plans best" Mr David yace "You!!" Shiru Abuturrab yyi, Mr David yace "And what's the name?" Abuturrab yace "Aliyu" Mr David ya girgixa kai yace "Ina ka kai min 'ya ta Aliyu, where did you take my daughter to, why did you part her away from us, imagine ur self in our shoes, kwatsam wataran wani ya xo ya rabaka da tilon 'yar ka just for his selfish own interest.... How will you feel Aliyu, me yasa xaka rabani da yar da ita kadai ke garen a duniya" tunda ya fara magana Abuturrab ya dafe kansa bai iya yace masa komai ba har ya kai aya, jin shirun yyi yawa Mr David yace "i knw u there....." da kyar ya iya bude baki yace "Abba kayi hakuri, nasan nayi kuskure kuma ina rokon gafararka, forgive me plss, komai ya faru duniya rubutatcce ne..... Ban taba tunanin xan aikata abinda na aikata ba ko da a mafarki ne, kuma nasan baxan so a min haka ba, ni bn yi abinda nayi da niyar cutar ta ba, ni musulmi....." Daga haka yyi shiru, Mr David dake saurarensa ya bude ido don tunda ya fara magana idonsa ke rufe, yace "A ina kuke ynxu?" Shiru Abuturrab yyi kafin a hankali yace "Gombe!" Mr David ya koma gefen gado ya xauna yace "Gombe?" Abuturrab bai ce komai ba, hakan yasa yace "Am asking u for this favour, plss ka dawo min da 'ya ta Aliyu am begging u in d name of God" Abuturrab ya girgixa kai yace "My dad... Baxan iya shigowa kano sbda shi ba" Mr David yace "In xo knn in karbi 'ya ta" shiru Abuturrab yyi, Mr David yace "Talk to me plss" Abuturrab ya d'an yi murmushi yace "Alryt Sir, sai dai Samantha matata ce a ynxu haka, i married her according to the teachings of my religion..." Kasa ce masa komai Mr David yyi, Aliyu ya lumshe ido a hankali yace "Xa mu yi farin ciki da xuwan ka gombe Sir, but please kayi mana favour daya, kada ka sanar da Mum komai plss sir, tsoronta ya sa Samantha kin kira all this while" A dai dai nan Rachael ta shigo dakin rike da kayan k'ari, Mr David ya dago ya kalleta, ta karaso inda yake ta ajiye kumallon tace "Ga shi nan naga baka sakko ba" katse wayar yyi ya ajiye yace "Ehh waya nake yi" xaunawa tayi tace "Anjima xan je kaduna fa" ba tare da ya kalleta ba yace "Me xaki yi a kaduna" tace "Ehh akwai wani taro da xan bude da addu'o'i, kuma ae na gaya maka yanda muka yi da priest ranan, don haka xan koma inji yaya" kallonta kawai yake, tana hararansa tace "Ya kke kallona haka malam, ni har gobe baxan fasa cewa baka wani damuwa da barin Samantha gida ba, bnda haka uba na gari ba sai inda karfinsa ya kare ba na ganin ya kubuto 'yar sa daga hannun matsiyacin d'an ta'adda, wai kunya? Kawaici? Toh Allah wadaran fulani, kuma wnn abinda na lissafo ne ajalinku, kawai sai ka tsaya yau heartache gobe heartache ka kasa cewa komai ka kasa daukan ko wani action, to God who made me... ni kam sai in dai jehovah ne ya dauki raina, amma sai nasa shegen yaron nn dana sanin dauke min 'ya ta, sai nasa an min duk abinda xa ayi ya bakunci lahira, ita kuma in har naga ya canxa mata ra'ayi ya cusa mata addininsa to gwara naje nayi layyarta a Jerusalem, i prefer her being killed har lahira kuwa...." Tana huci ta kare maganan, shi kam sai kallonta yake, can ya girgixa kai yace "As a true Christian kike bude baki kike fadin haka Rachael?" Mikewa tayi a fusace tace "So what? Sai in bari a cuce ni? Ni ynxu idan ba Jesus Christ xae sakko ya dakatar da ni ba bbu uban da ya isa hanani abinda ke raina" daga haka ta nufi kofa kamar xata tashi sama tana cewa "Ni naga kamar ma da hadin bakin ka a lamarin nn David, uban waye bai san fulani da shegen mugunta ba dama, ga kuma abinda priest yace har da sa hannun yan uwanka kuma nasan ba kowa bane kilan matsiyaciyar Maryam din nn ce, in kuma na gano itan ce wllh sai na daureta an bi min hakki na" daga haka ta fita ta banko masa kofa, wayarsa ya dauka ya nemo number kanwarsa Maryam ya kira ya kai kunne, yana fara ringing ta daga tace "An tashi lafiya yaya?" Yace "Lafiya Maryam ya gida da yaran?" Tace "Alhmdllh, jiya kuwa nake ta xuci xucin kiran ka Allah bai yi ba, Husnah tace min baka ji dadi ba, ya sis Rachael?" Lumshe ido yyi ya bude yace "Kar ki boye min komai Maryam, duk tambayar da xan maki ki bani amsata tsakanin ki da Allahn da ya halicce ki" Shiru tayi gabanta na faduwa, ya nisa yace "Maryam kinsan inda Samantha take ko baki sani ba?" Xuciyarta ya dinga bugawa da sauri cikin dakiya tace "Ban gane ba yaya, nasan inda take kamar ya?" Ya girgixa kai yana murmushin karfin hali yace "Nace ki fada min gaskiya yar uwa, kar ki ji komai" Hawaye ya cika idonta ita dai tasan har ynxu bata ci karo da mai hakuri da kawaicin yayanta ba, ba lallai ya ji haushinta ba ko da xata fada masa gaskiya amma ai da kunya ace tasan inda yar dan uwan nata uwa daya uba daya take, yar da ita ke nan masa duniya amma tayi shiru taki nunawa, muryarsa ya katse mata tunaninta yace "Ina sauraren ki Maryam" tayo gathering courage tana share idonta tace "Na sani yaya, amma ba don in cuce ka nayi shiru ba, ka yafe min yaya, kasan baxan yrda da duk abinda xai hallaka Samantha ba, just that komai ya faru a duniyar nn tsararre ne daga Allah, it's already written, kayi hakuri yayana" kuka ta fara yi, ya dafe kansa yace "Ya isa haka Maryam,ban ce ki min kuka ba," da kyar ta tsayar da kukan yace "Toh a ina take?" Tana share fuskarta tace "Samantha na gombe yaya...." Ya dago kansa yace "Toh shknn, dama sun kira ni daxu ita da yaron" Anty Maryam ta mike da sauri tace "Sun kira ka yaya?" Yace "Eh" D'an murmushin farin ciki tayi tace "Amma sis Rachael bata sani ba koh?" Yace "Bata sani ba" Ajiyar xuciya ta sauke tace "Toh naji dadi yaya, don Allah kar ka fadi mata" murmushi kawai yyi bai ce komai ba, murya can kasa tace "Sai dai fa yaya Samantha tayi aure, a nan maraban jos aka daura auren" bai iya yace mata komai ba, tasan bai ji ddi bne, ta kwantar da murya tace "Kayi hakuri yaya ka kwantar da hankalin ka, you know God plans best, irin ta mu kaddarar knn, sannan yaya Musulmi ba a abun ki bane a gun ka, don't forget our father was a muslim till death, so are his relatives, Beside ni naga yaron nn na yaba da hankalinsa kuma kasan daga irin gidan da ya fito, bbu wanda ya isa ya tsallake kaddararsa, shi ma nasan bai taba tunanim xae auri warce ba musulma ba, kuma wllh yaya yana sonta fiye da yanda kake tunani ita ma kuma tana son sa...." Shiru tayi jin shi ma yyi shiru, ya gyada kai yace "Shknn we will talk some other time Maryam" Tausayinsa taji sosai, hawaye ya xubo idonta tace "Amma xaka je gun nasu a gombe yaya" Yace "Xan je" tayi murmushi tace "Toh shknn yayana Allah yyi mana mai kyau" yace "Amin" daga haka ya katse wayar, tayi tagumi a xuciyarta tana roka ma yayan nata rahama a gun Allah. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By Khaleesat Haiydar📚✍🏻 78..... Da kyar Abuturrab ya samu ya lallashi Samha ta tsayar da kukan da take, cikin kwantar da murya yace "Beside Abba fa yace xai xo soon baby" a hankali ta dago tana kallonsa tace "Yaushe?" Yana share mata hawayen idonta yace "Soon yace min" daga haka ya rungumeta. Washegarin ranan da rana kiran Anty Maryam ya shigo wayar Abuturrab, ajiye drip din da yake hadawa xai sa ma Samha yyi, ya daga kiran suka gaisa, tace "Ashe kun yi magana da Abban Samha jiya?" Yace "Ehh Anty Mun kirasa" tace "Toh maa shaa Allah, naji dadi da kuka yi hakan, amma ya ku ka yi da shi?" Yace "He said he will be coming to gombe" Shiru tayi kafin tace "Toh shknn, Allah kai mu, ina babyna?" Kallon Samha dake kwance ta lullube da blanket har kanta yyi, yace "Ga ta Anty, bata da lafiya ne" Anty Maryam tace "Subhanallah, me ya sameta, tun yaushe?" Ya rasa abin cewa, can dai yace "Kwanan nan, bari in bata wayar" Anty Maryam da lkci daya ta gano dalilin ciwon tace "Toh bata wayar" karasawa yyi kusa da ita ya yaye bargon, ta bude idanuwanta a hankali, Ya kai mata wayar kunne yace "Anty xata maki magana wife" Cike da karfin hali Samha ta amsa kiran da Anty Maryam ke yi mata, Anty Maryam tace "Sannu Daughter, ya jikin" a hankali tace "Da sauki" Anty Maryam tace "Tun yaushe ne baki da lafiya?" Bata iya tace komai ba don ita ynxu magana ma burden yake xamar mata, hakan yasa Abuturrab ya mayar da wayar kunnensa, Anty Maryam tace "Ikon Allah, haka take jin jiki?" Yace "Da sauki Anty" Anty Maryam tace "Toh Allah ya sauwake, in shaa Allah ina nn xuwa dubata wnn karan" yace "Toh Anty, Allah ya kai mu" daga haka suka yi sallama ya ajiye wayar ya ci gaba da abinda yake. Bayan sati biyu ta ishesa ya kira mata Abbanta, bbu musu ya dau wayar ya nemo number ya kira, yana fara ring ya kai mata kunne ta karba, yayi tagumi yana kallonta don ramar tayi yawa, abu kusan wata uku amma ba sauki, "Hello, you call back ltr, he's nt around...." Muryar mum dinta ya d'aki kunnenta, a mugun tsorace ta sake wayar, yayi saurin dauka ya kai kunne shi ma yaji muryar ya katse kawai, ya mike ya ajiye wayar, can ya kalleta ya sakar mata murmushi ganin kuka take son yi, ya koma ya xauna yana shafa gefen fuskarta yace "Xaki fara aikin naki?" Ko tanka sa bata yi ba, yace "Xa mu je asibiti gobe baby...." Washegari da ya kasance Sunday yana xaune parlor kan laptop ita kuma tana daki as usual a kwance tana fama, bbu ynda bai yi da ita ba su tafi asibiti don yana son a mata scan amma taki wai bacci xata yi, fitowarsa knn daga dakin bayan ya tabbatar tayi baccin, danna bell aka yi ya mike ya isa kofar a tunaninsa khadija ce don ita kan xo a lkcn, Fatima ce tsaye bakin kofar, suna hada ido tace "Good afternoon" yace "Afternoon..." Tana jujjuya textbook din hannunta da handouts ba tare da ta kallesa ba tace "Pls idan baxan takura ka ba i need more explanation on this, am having test on it 2marrow in d morning, na samu Ummi tace min she's busy, Colleagues dina sun yi kkrin koya min but i seem nt to get it, and that's as a result of nayi missing lecture din ne shi yasa har ynxu ban gane ba, I've......" Katse ta yyi don surutun ya fara isar sa yace "What course?" Tace "Surg!" Juyawa yyi ya koma parlon ta bi bayansa, ya isa inda yake ya xauna yace "Me yasa baki kira Dr Shariff ba, nasan yana gida nd he will gladly come to assist you, ni gashi xa ki katse min aikin da nake yi" tace "I don't believe he even knows it" tabe baki yyo ya mika mata hannu ta basa litattafen hannunta, ya jawo table ya daura su kai yana dubawa, d'an xaro ido yyi tunawa da Samha da yyi ya kalli hanyar daki, can yace "Ohk, you sit let me make it fast xan fita ne" ta karasa ta xauna gefensa, nan ya fara koya mata course din yanda yasan xata fahimta, sai dai he's making it brief don Allah Allah yake ya kai karshe ta wuce sbda Samha, bai san tun da bell yyi ring ta farka ba, ita dai idonta na kan handout din tana saurarensa, Can yace "Wait! Are you getting me?" tace "Of course Noo, you re fast" yayi shiru yana kallonta, tace "i want you to teach me nt lecture" yace "But this is teaching nt lecturing madam" ta girgixa kai tace "Noo, ko in gwada maka ynda ake teaching?" Ya ajiye pen yace "Toh nuna min" sai a snn ta kallesa suka hada ido tun da ta shigo parlon, sauke idonsa yyi ta jawo takardan kusa da ita, nan tafara masa bayanin abinda yake mata, yayi shiru yana sauraronta, yyi mamakin bayanin da take with experience, fiye da ma ynda yake mata, ya girgixa kai yace "Dama kin iya kika kawo min?" Ta dago ta kallesa tace "Not at all, ynxun nn da ka fara min na gane...." Ya gyada kai bai ce komai ba, tayi murmushi tace "where you thinking I'm that dull?" Bai tanka ta ba, ta tabe baki tace "Toh ko kai baxa ka gwada min kkri a field dina ba..." Murmushin da bai shirya yi ba yyi yace "Really?" Bata kuma kallonsa ba, yace "What's ur point lst semester?" Tace "4.8 upward shi ne point dina tunda na fara karatu" dariya sosai ya dinga yi har da rike kai, ita kam sai kallonsa take, Mikewa xaune Samha tayi, dama tun shigowar fatima ta baxa kunnuwa tana saurarensu, ta cire bargon jikinta ta sauka kan gadon, har ta mance rabon da ta iya tsayawa ba tare da ta ga jiri ba, yau kam bata ji jiri ba, ta fice daga dakin, haba yana hangota dariyar ya makale a throat dinsa, bata ko kallesu ba ta nufi kitchen, sai ka rantse lafiyarta lau, Fatima dai ta gefen ido ta bi ta da kallo, shi kam mamaki ne ya ishesa don har ya mance rabon da ta taka har ta fito parlor da kanta, ya dai yi karfin halin jawo takardun ya ci gaba da koya ma Fatima, Tsaye Samha tayi kitchen duk ta rasa me ke mata dadi, taji xuciyarta na mata wani xafi, can kmr warce ta tuna abu ta juya ta isa gun da jarkan manja yake ta dauka, ta dawo ta dau pan ta xuba a ciki, ta kunna gas ta daura kai, ta dauki albasa da wuka ta yanyanka albasan ta xuba cikin man ta kara gas din sosai, ta ja gefe ta tsaya, kan kace me manjan ya fara soyuwa hayaki ya cika ko ina, ko gyaran murya bata yi ba ita da ke tsaye cikin hayakin, sai da taga man yana hayaki ssai ta juya ta fice, kofar parlor ta wuce, fatima dai ta fara gyaran murya tana rurrrufe ido jin hayakin na choking dinta, shi kam bin ta yyi da kallo ta kulle kofar da makulli ta cire makullin ta wuce daki, lkci daya fatimata fara tari sosai ta sauko daga kan kujera, ya mike da sauri shima jin hayakin, ya kalli kitchen yaga ta nn yake fitowa ya karasa da sauri ya shiga ciki, da kyar ya karasa gun gas din don shi ma har ya fara tarin sosai ya kashe gas din ya sauke pan din kai, ya fito, durkushe yaga fatima numfashinta na neman seize, ya karasa da sauri yana furta inalillahi ya dagota saketa yyi ya isa kofa ya murda ya ji sa a rufe, dawowa yyi ya sake daga ta yyi cikin spare room da ita ya rufe kofar sbda hayakin kar ya shigo, yana xaunar da ita ya sake fita, dakin Samha ya shiga ya ganta kwance ta lullube ya cire bargon yace "Me kike soyawa a kitchen Wife?" Ta kallesa a takaice tace "Manja!" yace "Me xa kiyi da shi?" Ta mike xaune tace "Sha xan yi" rasa abinda xae ce mata yyi, ta koma ta kwanta ta juya masa baya, kwantar da murya yyi yace "Toh bani makullin in bude mata ta tafi baby, kinga Asthman ta ya tashi" juyowa tayi ta sake mikewa xaune ta watsa masa wani kallon da ya sa hanjin sa kadawa, cikin daga murya tace "Baxan bayar ba, uwar me ya shigo da ita gidan??? Kai ka sa ta a boko ko kayi mata kama da lecturer?" K'asa cewa komai yayi ya dinga kallonta yana mamakin inda ta samu strength din masifa haka, yarinyar da da kyar take bude baki tayi magana, xama ma sai ya dagata take iya yi, ta mike tsaye tana huci tace "Toh nace baxan bayar da makullin ba ko baka ji ba?" juyawa yyi bai ce komai ba ya nufi kofa, ta murguda baki tace "Next time idan ance ta shigo gidan mutane unnecessarily baxata sake ba" daga haka ta koma ta kwanta. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 79..... Bedroom dinsa ya koma ya fara duba spare key, yana gani ya dauka ya fita parlor ya bude kofar snn ya koma dakin da fatima take, har dai lkcn numfashinta bai dawo dai dai ba sai dai ba kamar daxu ba, ya isa kusa da ita yace "Sorry pls, ta mance you re asthmatic ne she wouldn't have done that" daga haka ya mika mata hannu ya dagata yace "May be later xan xo in karasa maki, or you talk to Mami" bata ko kallesa ba ta sa mayafin jikinta ta rufe hancinta ta fita dakin ya bi bayanta, takardunta ta kwasa a parlon ta nufi kofa yana biye da ita a baya, tana fita parlon yace "Sai kiyi amfani da inhaler idan kin shiga gida" ba tare da ta kallesa ba tace "Thanks" tayi gaba abunta, ya juya ya koma ciki ya rufe kofar snn ya wuce dakin Samha, kwance ya sameta ya rungume hannayensa yana kallonta, can ya girgixa kai yace "Toh tashi ki shirya mu tafi asibiti tun da kin samu strength" bata juya ba bare tace komai, ya isa kusa da ita ya xauna yace "Kin ji Baby" tace "Ni ba iyawa xan yi ba" dariya ta basa, ya dai yi murmushi kawai yace "Kamar ya baby?" Tace "Ina jin jiri" ya wara ido yace "Toh daxu da kika fito baki ji ba knn?" Mikewa tayi ta daure fuska tana kallonsa tace "Ehh" ya kwantar da murya yace "A'a ba fada bane wife, daure ki shirya mu je a duba mana babynmu" wani kallo ta masa ta koma ta kwanta. Ya mike ya fiddo mata da kaya, da kyar ya lallabata ta shirya yana taimaka mata, sai bayan da ta huta don ce masa tayi ta gaji snn ya kama hannunta suka fita yana rike da makullin mota, yana bude mata mota ta shiga ta rufe tana mayar da numfashi, shi dariya ma take basa, ya xaga ya shiga maxaunin driver yyi warming motar snn suka bar gidan. Sai bayan azahar suka dawo gida daga clinic din, nan parlor ta kwanta yace "Baby da ki daure sai ki karasa ciki mana" juya kanta tayi bata kulasa ba, yace "Uhm! Toh Allah baki hakuri" Daga haka ya dau makullin mota da takardan scan din ya shiga bedroom dinsa, yana tsaye gaban mirror ya sake warware takardan hannunsa, murmushi yyi yace "Babies...." Ajiye takardan yyi ya juya ya koma parlor, har ta fara bacci ya sameta, a hankali ya dagota da niyar kai ta daki ta bude ido, da sauri yace "Baby you re nt comfortable here kar wuyan ki yyi ciwo" Mikewa xaune tayi tace "Xan iya da kai na" ya saketa ta mike ta yi hanyar daki kmr warce iska xai kade ta fadi, underneath his breathe yace "Is it the pregnancy that's making her furious all the time" tana isa kofar dakinta ta duka, ya mike ganin haka, tana ganin ya nufo ta ta mike ta bude kofar ta shige ta rufe, dariya ta basa ba kadan ba ya koma ya xauna yace "Xaki neme ni anjima ai" Washegari da safe tana gama amai tace masa ita gari take son sha, ya d'an bude ido yace "Gari kuma baby" ta kwanta tace "Ehh" kallonta yake ya ma rasa abinda xai ce mata, can dai yace "Toh ina xa mu samo gari da sassafen nn" hannu ta buda masa alamar bata sani ba, yace "Toh baby ki bari da rana sai in nemo maki kinga ynxu it's too early" bata ce komai ba, yace "Toh me kuma xaki ci?" A takaice tace "Nothing" ya kafa mata ido, can ya mike ya shiga daki ya dau makullin mota ya fita nemo gari, sai kusan karfe goma ya dawo, yana parking Ummi na fitowa xata clinic, ya karasa ya gaisheta tace "Morning, ya mai jiki? Hope she's improving" Yace "Ehh Mami da sauki," tace "Toh kun yi scan ma kuwa?" Yace "Jiya muka je clinic" tace "Maa sha Allah, Allah ya kara mata lfya" yace "Ameen Mami, Allah ya tsare hanya" tace "Ameen boy," daga haka ta shiga mota, ya juya ya bar gun, bacci ya tadda Samha take, ya ajiye garin ya durkusa kusa da ita yace "Baby to gashi na samo maki..." Ganin kmr baccinta yyi nisa ya kyaleta ya fita dakin. Haka suka ci gaba da rayuwa Samha kullum masifarta karuwa yake, har wani shakkarta ya dinga ji don in ta masa wani tsawa har cikin kansa yake ji, gashi shi bai son hayaniya, abu kadan ke bata mata rai, ko kadan bai jin haushin hakan sbda condition dinta duk da dai ba kamar da ba don ta fara samun kanta, wani lkcn ta kan ci abinci ko kadan ne, amai kuma bai fi tayi sau daya a rana ba, kyanta ya kara fitowa sosai, sai dai ramar da tayi yyi yawa, bai gajiya da xama yyi ta kallonta don abubuwanta dariya suke basa, ganin she's getting her self ya fara fita aiki duk yamma ya dawo karfe takwas, yau ma yana clinic wajen karfe shidda wayarsa dake kan table ya fara ring, bai dauka ba sbda patient dake gabansa har wayar ya katse, bayan ya sallami patient din ya dau wayar ya ga Anty Maryam ce ta kirasa, bin kiran yyi tana dagawa suka gaisa ta tambayesa Samha da jiki yace "Alhmdllh da sauki Anty" tace "Toh Allah kara mata afuwa, kila in taho gobe idan Allah ya kai mu" yace "Toh Allah kawo mana ke lafiya Anty" daga haka suka yi sallama ya ajiye wayar, tunawa yyi da plantain chips da chocolates da Samha tace ya siyo mata, ya kalli agogo yaga shidda ya d'an gota, yyi deciding kawai yyi magrib snn ya wuce, mikewa yyi ya dau file dake gabansa ya fita office din don xuwa office din Ummi, Ummi na xaune sai Dr sharif dake xaune yana facing dinta Fatima kuma na kwance kan 2 seater, ya ajiye file din hannunsa ya kalli fatimar, har ya mance rabon ya ganta don tafi xaman hostel kan gida, ganin yanayinta yace "Bata da lfya ne Mami?" Ummi tace "That's her cup of tea, ni baxata daura min tension dinta ba, is she the only Asthmatic patient, kullum sai ta jangwalo ma kanta ta xo tana daura min wahala, is she a kid?" yyi murmushi yace "Kiyi hakuri Mami, it's nt her fault...." A fusace tace "It's nt her fault kmr ya, is she big enough nt to be going around with face mask, inhaler kuma ynda kasan needle haka yake a gun ta, kullum sai ta sa ni cacan inhaler, ajiya take ban? Ko Rabi'a baxa ta min abinda take min ba," Dr Shariff yace "Kiyi hakuri Dr" Abuturrab ya kalli Fatima yace "Me yasa baki yawo da mask" ko kallonsa bata yi ba, yyi murmushi yace "Allah ya sauwake, bari mu je masallaci Mami" daga haka suka fita da Dr shariff, ana idar da sllh ya dawo yace ma Ummi xai koma gida, tace "Toh ku tafi da fatima am nt leaving now" sai da gabansa yyi mugun faduwa tunawa da Samha da yyi, ya dake yace "Toh Mami" daga haka ya kalli fatima yace "Mu je" snn ya juya ya fita, har ya ja motar ya fita daga clinic din gabansa bai daina faduwa ba, har suka yi nisa bai ce ma Fatima komai ba, ya dai tsaya yayi taking excuse ya fita ya siyo plantain chips da chocolate da Samha tace masa snn suka dau hanyar gida, yana isa gate yayi parking yana kallonta yace "Ohh i forgot bn gama siyayya ba, ki shiga ciki xan juya" bude motar tayi ta fita, ya ja motar ya bar gun, ajiyar xuciya ya sauke, yana isa gun masu sayar da fruits yyi parking ya sauki ya siya fruits din da xai siya ya koma mota, Kitchen ya same Samha, yyi mamakin hakan ssai, yana tsaye bakin kofa yace "Baby me kike yi nan" ta juya ta kallesa kamar xata yi kuka tace "Yunwa nake ji" Yace "Toh me xa ki ci?" Ta bude ruwan dake tafasa kan gas tace "Ni indomie xan dafa" ya wara ido yace "Ohh that's nyc baby" dukawa tayi ta fiddo kwalin indomien ta ciro daya yace "Just one?" Bata tanka sa ba ta mike tsaye, yana tsaye yana kallonta har ta gama dafa indomien da ta cika ma uban yaji, ta daura kwai biyu a wani tukunyar, murmushi yyi yace "Baby duk wnn yajin" bata tanka sa ba still sai daure fuska da tayi wato ya fara isarta, hakan yasa ya ja bakinsa yyi shiru, tana xuba indomien a plate ta jira kwan yyi ta kashe gas din ta 6are ta daura kan indomien snn ta dau abinta ta juya, hanya ya bata ta fita snn ya bi bayanta, tana ajiye indomien ta dauko ruwa a fridge ta dawo ta xauna, ganin kallon da yake mata tace "Xaka ci ne?" Yace "Bayan daya kika dafa" tace "Toh ai baka ce min xaka ci ba" Yace "Koh?" Tace "Ka xo ka ci idan xaka ci mana" murmushi yyi yace "Tohm let me just taste" daga haka ya mike ya taho inda take ya debi abincin kadan ya kai baki, ji yyi kansa ya dauka tsabar yaji, ya mike yana girgixa kai yace "Yayi dadi sosai" daga haka ya bude fridge ya dau ruwa ya wuce daki. Washegari da ya kasance saturday karfe goma saura Samha ta tashi, shi kam dama tun da yyi Sllhn Asuba bai koma ba yana kallon wani movie a laptop, tana fitowa daga daki kitchen ta nufa, ya bi ta da kallo yace "Baby ina kwana?" Juyawa tayi ta kallesa ta d'an turo baki tace "Ina kwana" murmushi yyi yace "A'a ki amsa dai, ni kam duk an canja min babyna" bata tsaya ba tayi shigewarta kitchen, yana jin tana ta 6uruntun ta a kitchen ya kuma san abinci take dafawa don aroma din ya baibaye gidan gaba daya, bayan kusan minti talatin ta fito rike da bowl madaidaici a hannu, sae kallon bowl din yake yana son sanin me ta dafa, ganin xata wuce daki yace "Baby me kika dafa?" Ta juyo tace "Xaka ci ne?" Ya girgixa kai yace "A'a" tace "Porridge na irish nayi" bai ce komai ba, ko me ta tuna sai kuma ta dawo parlon ta xauna ta tankwashe kafa ta fara cin Irish din da yaji nama, duk da abincin ya shiga ransa sau daya ya kalla bai kuma kallo ba ya mayar da hankalinsa kan movie din da yake kallo, sai da tayi rabi ta ture bowl din, ya kalleta yace "Kin koshi ne" Bata ce komai ba ta jinginar da kanta da kujera, bayan kusan minti biyar ta mike da sauri, ya bi ta da ido, toilet dake parlon ta shige ta fara kwarara amai, ya mike ya bi bayanta, yana tsaye kanta har ta gama ya bude mata tap ta wanke bakinta snn ta fito, gun abincin ya ga ta koma ta xauna ta ci gaba da ci, bai ce mata komai ba ya xauna gun laptop dinsa, sai da ta cinye abincin gaba daya snn ta kallesa tace "Toh kai kayi breakfast din ne?" Yace "Kin ban ne?" Tace "na yi xaton ka ci" ta mike xata daki ta kwanta yace "Dear xamu yi visitor yau fa" Ta kallesa tace "Su wa ne?" Ya d'an yi shiru kafin yace "Aunt dita ce ita ma, tana son ta gan ki" Samha tace "Toh Allah ya kawo ta lafiya" yace "A siyo take away kawai koh?" Ta girgixa kai tace "A'a xan iya girkin" *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 80..... Samha bata iya ta karasa girkin tuwo da miyar ganye, sai jollof din da ta fara ba ta dinga jin jiri da tashin xuciya, bedroom ya wuce da ita ta kwanta, da damuwa yace "Sannu baby shi yasa nace mu siyo take away kika ce xa ki iya" bata ce komai ba sai rufe idonta da tayi, ya langwabar da kai yace "Bari in kira khadija ta karasa maki ko baby..." Bude ido tayi tana kallonsa, yace "Yau Saturday nasan she's at home" bata ce komai ba ya mike ya fita, Ummi kadai ce xaune parlor tana kallon wani program, ya xauna suka gaisa snn yace "Mami khadija na nan don Allah" tace "Ehh tana ciki" yace "Dama Samha ce ta fara girki kuma bata iya ta karasa ba...." Ummi tace "Ayya, toh bari ta fito ta karasa mata" daga haka ta kirawo khadija tace "Dear ki tafi ki taya Samha aiki kin ji" Khadija tace "Toh" daga haka suka fita tare da Abuturrab da yyi ma Ummi gdya, Khadija na shiga kitchen din ta ci gaba daga inda Samha ta tsaya shi kuma ya shiga dakinsa, waya ya dauka ya kira Anty Maryam tana dagawa suka gaisa yace "Kin taso kuwa Anty?" Tace "Eh tun safe na taso Aliyu, mun ma yi nisa" yace "Toh Allah ya kawo ku lfya, ya kiyaye hanya, idan kun iso park sai ki kirani xan xo in dauke ki" Tace "Ameen Aliyu, Alryt xan kira ka" yana ajiye wayar ya fita ya shiga dakin Samha ya sameta tana bacci, ya kalli agogo ya daura hannu fuskarta a hankali yace "Dear baxa ki daure ki shirya ba kafin Aunt din tawa ta xo?" Da kyar ta bude ido tana kallonsa, ya sakar mata murmushi yace "Yes, ki daure kin ji babyna, ko in taya ki wankan?" Gyada masa kai tayi, ya dagota xaune ya cire mata yar rigar baccin jikinta ya shiga bayi da ita. Abaya ya fiddo mata bayan sun fito bayin, ya shafa mata lotion ta sa kayan snn ya daure mata gashinta da ribbon ya fesheta da turare yana murmushi yace "Kin yi kyau wife" hararansa tayi ta kwanta, kafin karfe daya Khadija ta gama girkin ta wuce. Yana kwance gefen Samha dake bacci yana kallo a tv wayarsa yyi ring, ganin Anty Maryam ce ya mike xaune ya daga, tace "Aliyu mun iso fa" yace "Toh gani xuwa Anty" daga haka ya tashi yana kallon Samha, bai tasheta ba ya dau makulli ya fita, uku da yan mintuna ya isa park din, da fara'arsa ya nufi Anty Maryam dake tsaye rike da hannun autarta ya gaisheta, ta amsa da murmushi tace "Mun same ku lfya" ya duka ya dau kyakkyawar yarinyar da baxa ta wuce shekara hudu ba yace "Pretty how are you" yarinyar tace masa "Fyn" ya wara ido yace "Waow, then what's ur name" kallon uwarta tayi, Anty Maryam tace "Have u forgotten ur name?" Yarinyar tayi dariya tace "I am Ihsan" shafa kanta yyi yana murmushi yace "Welcome little Ihsaan" daukar jakarsu yyi yace "Anty ga mota can" Anty Maryam tace "Okay" daga haka suka nufi motar ya bude mata baya ta shiga ya mika mata ihsaan snn ya rufe motar ya xaga ya shiga maxaunin driver, suna isa gida yyi parking ya juya yana kallon Anty Maryam murmushi dauke fuskarsa yace "Anty bata san fa ku ne bakin da xa su xo ba" tayi dariya tace "Au haba" ya bude motar yace "Wllh kuwa Anty" bude motar tayi ta fito da ihsaan ya dau kayansu yace "This our home Anty" Tace "Maa sha Allah, Allahu ya ci gaba da hada kanku" yace "Ameen Anty" tana biye da shi suka wuce balcony ya bude kofar parlorn suka shiga, Xaunawa Anty Maryam tayi da autarta, ya nufi fridge ya dauko masu ruwa da drink da cups ya ajiye ya xuba masu ya mika ma Ihsaan nata yace "Take pretty" Karba tayi tace "Thank you" yana kallon Anty Maryam yace "Anty ga ruwa bari in taso ta, bacci take" daga haka ya wuce daki, har lkcn kuwa baccinta kawai take, ya xauna kusa da ita ya dinga shafa mata fuska a hankali yana jan hancinta, ta bude lumsassun idonta tana kallon sa, yace "Baby har yanxu baccin dai" murya can kasa tace "Am very hungry" Yace "Toh muje ki gaida aunt din tawa sai ki ci abinci" Da sauri ta mike xaune tace "Ta xo?" Yace "Yea naje park na daukota yanxu" kamar xata yi kuka tace "Ae ban ma gama girkin ba doctor" yace "Khadija ta karasa maki dear" Shiru tayi bata ce komai ba ya mike ya dagota ta tashi tsaye ya bata veil din abayar ta yafa a kai, kallonta yake ganin yanda Abayar ya fito mata da cikin jikinta sosai, yaga tayi masa kyau ba kadan ba, kallon kanta tayi ganin irin kallon da yake mata ta daure fuska ta koma ta xauna tace "Ni baxan iya fita da kayan nan ba" Ya wara ido yace "Me yasa baby?" Tace "Bana so" yace "Ya fa maki kyau sosai dear plss mu je haka tana ta jira fa" kmr xata yi kuka tace "Ni baxan iya ba" yace "Toh sbda me" tace "Ni dai Hijab xan sa" murmushi yyi yace "See you, to ance maki bata da ido ne, ko me xa ki sa ai ba boyuwa abinda kike boyewa xai yi ba" kallonsa take kmr xata yi kuka ta wani hade rai, yyi dariya ya dagota ya rungumeta ta baya yana shafa cikin yace "Baby plss mu je tana ta xaune parlor fa ita kadai" daga haka ya kama hannunta suka fita tana nonnokewa ita a dole kunya, suna shigowa parlon ta tsaya cak tana kallon warce ke xaune tana kallonta murmushi dauke fuskarta, wani kara tayi ta nufeta a guje, har cikin ransa yaji uban tsallen da ta daka, ita kanta Anty Maryam sai da tace "Ke kina da kai kuwa Daughter" bata ko saurareta ba ta fada kanta ta kankameta tace "Antynahh dama ke ce" Anty Maryam tace "Xa ki ji ma kan ki ciwo fa, kina da kai ma kuwa" Shi kam sai kallonsu yake, can ta sake Anty ganin Ihsan ta rungumeta ita ma tace "Anty me yasa baki taho da Asiya da Farouq ba" Anty Maryam tace "Suna gun grannynsu" Rasa inda xata sa Auntyn tata Samha tayi da ganinta tayi farin ciki ne ba na wasa ba, duk sai Anty Maryam taji tausayinta barin ynda taga ta rame, ganin ba kyale Antyn xata yi ba Abuturrab yace "Anty ku yi sllh ku ci abinci, kun kwaso hanya fa" Sai a snn Anty Maryam ta yakice ta jikinta ta mike suka wuce daki, har bedroom ya kai masu abincin don bai ga alamar Samha xata yi hakan ba, Anty Maryam tayi dariya tace "Aliyu kai ne da wahala haka" yyi murmushi yace "Toh Anty naga taki kawo maku ne, kuma da ita ke jin yunwa bbu me kwanciyan hankali sai ta ci" Samha dake jikin Anty Maryam ta daure fuska ta turo baki, ya juya ya fita dauko sauran abincin, Anty Maryam tace "Ji shashanci daga yana maki wasa sai ki hade rai ki cunno baki gaba" tace "Bana son wasan" Anty Maryam tace "Toh ina laifinsa, naga dai duk ni yake ma hidimar ko baki ji dadin hakan ba" tace "Toh ai nima nayi masa da nasa yan uwan suka xo" Anty Maryam ta hade rai tace "Toh ya ishe ki bana son fitsara, yaushe kuma kika xama fitinanna" Samha bata ce komai ba ta dauke kai, a haka Abuturrab ya shigo ya samesu ya ajiye abincin yace "Ga shi Anty, ku ci abinci" Anty Maryam tace "Sannu Aliyu nagode" satan kallon Samha yyi ya fita, ba dau lkci ba ya dawo kuma rike da plate din abinci ya ajiye gabanta yace "Kin ce kina jin yunwa ga abinci" kallon abincin tayi tace "Am nt any longer" Ajiye ma Ihsan abincin yyi yace "Pretty ke ki ci" Anty Maryam dai kallonta kawai take ganin har lkcn ita fushi take, murmushi kawai tayi ganin condition dinta ta kuma san ba laifinta bne, tunanin irin abubuwan da uwarta tayi lkcn da take dauke da cikinta take da irin wahalan da ta sha, can tace "Daughter daga magana sai fushi, to yi hakuri" ita dai bata ce komai, har Anty Maryam ta gama cin abinci Samha na xaune ta xuba ma tv ido, Anty Maryam tace "Yauwa daxu kin ce min yan uwansa sun xo?" Sai a snn Samha ta kalleta tace "Ehh" Anty Maryam tace "Amma bnda Mum dinsa koh?" Tace "A'a kanwar mum dinsa ce sai sisters dinsa biyu" Anty Maryam tace "Ayya, did they stay long?" Ta girgixa kai tace "Just 2 days suka yi" tace "But are they okay" Samha ta kwantar da kanta tace "Yes his mum sis is very kind, har da zinari ta ban na dan kunne, sisters dinsa kawai ne basa so na" a hankali ta kare maganar, Anty Maryam tace "Don't worry duk xa su so ki kin ji Daughter, everything is just time" Daga haka suka dinga hira har aka kusan Magrib, shi kuma Abuturrab yana bedroom dinsa da Ihsaan suna kallon cartoon, yana yin alwala yace "Pretty kije Mumy ta sa maki cartoon a can dakin xan je masallaci" tana fita ya wuce masallacin, Anty Maryam na idar da sllh ta kalli Samha tace "Ke ko ki d'an yi kara ki dinga yin sllh bakya yi koh?" Samha ta kalleta tace "Anty ae baya cewa in yi" Anty Maryam tace "Sai yace maki daughter," murmushi tayi tace "Toh xan na yi Anty" Anty Maryam tace "You still don't have interest in joining us koh" tana murmushi tayi maganar, Samha tayi dariya tace "Uhm Anty ae bance haka ba fah" Anty Maryam tace "Ko akwai abinda yake maki that's prohibited in Christianity?" Kmr xata yi kuka tace "Eh mana...." Anty Maryam ta d'an yi shiru tana kallonta, sai kuma a hankali tace "Gaya min me yake maki Samantha?" Ta turo baki bata ce komai ba, Anty Maryam tace "Noo ki gaya min kar ki ji komai" *Haske writers asso* [11/27, 7:18 PM] ‪+234 703 709 9528‬: 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 81...... Kamar xata yi kuka tace "Toh ba sai yayi ta kula mutane ba...." Anty Maryam tace "Su waye mutanen?" Dauke kai tayi ta ki cewa komai, Anty Maryam tace "But don't forget his profession, kin ga kuwa ae shi na mutane ne Samantha, beside where in d bible aka ce kar a dinga kula mutane?" Tace "Toh Anty fa sai yarinyar ta dinga xuwa nan tana kawo masa assignment yana yi...." Anty Maryam tace "Wace yarinya ce?" Tace "Our neighbor mana" shiru Anty Maryam tayi kafin tace "Da ya san su ne?" Tace "I don't know for him" murmushi Anty Maryam tayi tace "Ke dai dama har da guntun masifar ki" Samha bata kuma cewa komai ba, Anty Maryam tace "Kun yi waya da Abban ki ashe" dawowa kusa da ita tayi da sauri tace "Eh Anty, kuma yace xai xo, yaushe ne xai xo?" Anty Maryam tace "Xai xo amma ba yanxu ba daughter" Samha tace "Sbda me Anty? ina son in gansa" lkci daya hawaye ya cika idonta, Anty Maryam ta dafa shoulder dinta tana yar dariya tace "Xai xo mana, may be to see his grandchild, kinga that's the right time ma koh?" Tuni Samha ta sunkuyar da kai, Anty Maryam tace "Ko ba haka Daughter?" Turo baki tayi ta mike ta kwanta kan gado, Anty Maryam tace "Idan bacci xa ki yi ki tashi ki tafi gun mijin ki" ba tare da ta kalleta ba tace "Ni a nan nake kwana Anty" Washegari Anty Maryam na idar da sllh bata koma bacci ba, tayi wanka snn ta fito parlor, xaune ta tadda Aliyu laptop gabansa, yana ganinta ya katse abinda yake yi ya gaisheta tace "An tashi lfya?" Yace "Alhmdllh Anty" xaunawa parlon tayi yace "Anty amma sati xa kiyi mana koh" tace "Gobe xa mu juya in sha Allah Aliyu, ae an yi xumunci" yace "Anty gobe fa kika ce" tayi murmushi tace "Toh na bar yara gida ai" yace "Kince gun grannies dinsu suke ai" tayi dariya tace "Ehh duk da haka, amma ae tunda mun ga waje xa mu dawo wani lkcn" yace "Toh Allah yasa Anty" tace "Aliyu har ynxu baka ka making effort na ganin ka ja ra'ayin samantha koh" kallonta yake jin abinda tace, can dai yace "Anty bana son taga am forcing her into it" Anty Maryam ta girgixa kai tace "Noo it's nt by forcing her, actions dinka xai dinga jan ra'ayinta mana, infact ba actions kadai ba, time to time yana da kyau ka dinga fada mata do's nd don't's din addinin ka, ka dinga nuna mata islam is nothing but peace, ka nuna mata muhimmancin addinin ka" jin yyi shiru ta ci gaba tace "Misali kana sllh a kan lkci, kana karatun qur'an lkci lkci a inda take, infact u make it ur normal routine, u re educated Aliyu ba sai na gaya maka wa ennan abubuwan ba, a k'ashi dari nasan Samantha ta san meye musulunci k'ashi 40, ai ta xauna da ni, har sllh tana yi idan tana gu na, islamiyya ma kullum tana xuwa sai dai ranan da babu, Idan ka kula ba wai tayo xurfi a Christianity din bane, uwarta ce ke tusa mata ta karfi, yeah Abbanta is a Christian amma sai in ce maka shi church din ma ba xuwa yake ba, xai dai yi karatun littafinsu a gida idan yana ra'ayi...." Abuturrab ya sauke ajiyar xuciya a hankali yace "Haka ne Anty, am nt making any effort into making her fall for islam don kwanki ita da kanta tace tana son in sa ta islamiyya daga baya kuma tace baxa ta je ba, kuma Anty hakan baxai yiwu ba ynxu sbda condition dinta....she's totally changed" Anty Maryam tayi murmushi tace "Sai hakuri, kuma naji ddin da ka fahimci cewar abinda take ynxu ba halinta bane kuma ba yin kanta bane, ban mancewa haka uwarta tayi tana da cikinta don lkcn ina wajensu, ka ci gaba da hakuri har Allah ya raba su lfya" yace "Toh Anty, nagode" tana murmushi tace "Na tambayeta ko akwai abinda kke yi that's contrary to her religion tace eh" xaro ido yayi yace "Me tace ina yi Anty?" Dariya Anty tayi tace "Cewa tayi kana kula mutane" bai san lkcn da yyi dariyar ba shi ma, yace "Anty kinsan kishin Samha yyi yawa, she's making me get frightened with her type of jealousy, kinga just yarinyar neighbor dinmu ce fa wani time din ta kan kawo assignment in duba mata, kuma mum dinta ce ta ban aiki clinic dinsu, so i just can't say No, ban san ynda xan dinga avoiding yin assignment din ba..... Ko me xan ce ma Samha baxa ta taba fahimtata ba, mamakin kishinta nake" Anty Maryam ta girgixa kai tace "Toh Allah ya kyauta ka dai bi ta a hankali har ta sauka lfya, tsabar jaraba ne ke damunta, though ba halinta bane, kishi kuma gado shi tayi gun Uwarta" yayi murmushi yace "Haka ne Anty" sai kusan karfe tara Anty ta shiga kitchen don girka breakfast duk da Abuturrab yyi niyyar fita ya siyo ta hanasa, Hajiya Samha kam tana ta bacci daki da Ihsan, kafin karfe goma Anty Maryam ta gama komai, ta tsaftace kitchen din snn ta fito. Da rana Abuturrab ya fita ya yo masu take away na lunch, Anty Maryam na ba Ihsaan abincin ta kalli Samha dake shan gari tace "Daughter ki bar garin nn haka ki ci shinkafa" ta girgixa kai tace "A'a Anty" Anty Maryam tace "Kina ji na?" Kallonta Samha tayi, tace "Daga yanxu ki dinga sllh ba sai ance kiyi ba" Shiru tayi kafin tace "Toh Anty" Anty Maryam tace "A ko da yaushe fa ba wai idan kinyi zhur baxa ki yi Asr ba" tayi murmushi tace "Toh xan na yi Anty" Anty Maryam tace "Yauwa my daughter, don kinyi addinin kakan ki ae ba laifi bane" Murmushi Samha ta kuma yi bata ce komai ba, Anty Maryam tace "Ko baki sha'awar addinin?" Nan ma murmushi tayi bata ce komai ba, Anty Maryam tace "C'mon talk to me" yar dariya tayi tace "Ina yi mana Anty, kema kinsan i love sallat, kuma akwai time din da doctor ya karanta mani wani verse a bible da yake ce min jesus christ acted like Muslims do, he fall with his face to ground when praying, nd truely Matthew 26:29 said 'Going a little further, jesus fell with his face to the ground and prayed.... And i knw till date d Coptic Christians nd the jews in the holy land still pray d way Jesus did" Anty Maryam tayi murmushi tace "Am happy u kept this at the back of ur mind, amma yaushe ya karanta maki verse din?" Tace "Ya dade fa, ae da yana yawan kawo min verse kawai dainawa yyi" Anty Maryam tace "Do you believe in prophet Muhammad Pbuh?" Samha tayi shiru bata ce komai ba, Anty Maryam tace "You remember this verse 16:5-8.... 'for if i go not away, the comforter will not come unto you, but if i depart, i will send him unto you, and when he comes, he will reprove d world of sin and approve righteousness nd judgement...." Kallonta kawai Samha take, Anty Maryam tace "Who is this comforter?" A hankali tace "The Holy spirit" dariya Anty Maryam tayi tace "Holy spirit ne xai yi reproving world yyi approving righteousness nd judgment? Da can ance maki bbu holy spirit din, Jesus Pbuh was referring to prophet Muhammad S.a.w, an san gaskiyan ake dannewa" ita dai Samha bata ce komai ba, Anty Maryam tace "Doctor din bai taba maki tarihin Prophet Muhammad ba?" Girgixa kai Samha tayi, tace "Toh ki ce ya baki tarihin" a hankali Samha tace "Toh" Sallama Abuturrab yyi ya shigo dakin bayan Anty ta amsa ya durkusa yana wasa da Ihsaan yace "Anty pls xa mu je gun neighbour dinmu ku gaisa, the woman is very kind, nd she's a frnd to my mum" Anty tace "Allah sarki, to bari mu je" mikewa yyi ya dau abincin Ihsan ya daga ta suka fita parlor, Samha ta turo baki, Anty Maryam tace "Toh what's the pouting about kuma ynxu" tace "Ko kallona fa bai yi ba" dariya Anty Maryam tayi tace "To ai ba wajen ki ya xo ba, ya kalle ki kuma yyi laifi tun da naga masifa tsabagenta kike ji da fitina ynxu" Mikewa tayi ta haye kan gado, Anty Maryam ta tabe baki ta mike ta dau hijab din ta ta nufi kofa tace "Aiki ya samu masu shi" daga haka ta fita, Da fara'a Ummi ta tarbi Anty Maryam ta sa Usaina ta kawo mata drinks ta dau Ihsaan tana tambayarta ya take, sun d'an taba hira kafin Anty Maryam suka fita parlorn da Abuturrab ta bar ihsaan. Washegari da safe Anty Maryam ta fara shirin komawa kd, Samha ta dinga rusa kuka ita sai ta bi ta fa, shi dai bai samu bakin cewa komai ba, Anty Maryam ma ta fita harkanta don ji take kmr ta make ta, bbu ynda bai yi da ita ta taho su tafi tasha ba amma taki, Sai da Anty Maryam xata fita taji tausayinta, ta dawo ta durkusa kusa da ita tace "Haba daughter, u re married yanxu fa bai kamata kina behaving kamar karamar yarinya ba, kuma na fa ce maki soon xan dawo, ko baki son in xo in xauna da ke idan kin haihu?" Ita dai Samha bata ce komai ba sai hawaye take, shafa kanta Anty Maryam tayi tace "Toh kiyi hakuri, tashi ki raka mu park" girgixa kai tayi alamar baxata je ba, cike da tausayinta Anty Maryam ta bar parlon Abuturrab ya wuce da ita park, shi ya biya kudin motar duk da bata so hakan ba, har ihsaan sai da ya biya mata seat snn ya bata dubu goma a hannu, bai saurare Anty Maryam dake cewa ya karbi kudinsa ba, ganin ta dage yace "Haba Anty, ni fa ihsaan na ba" sai da yyi da gaske ta hakura, yana tsaye har motar ta cika suka tashi snn ya nufi motarsa ya koma gida. *Haske writers asso* [11/27, 7:53 PM] ‪+234 703 709 9528‬: 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 82..... 3months later. Samha na daki kwance misalin karfe daya na rana sai juye juye take tsabar yunwar dake cinta gashi ta ki tashi, shi kam Abuturrab na kwance parlor da yake ranan lahadi ce yana kallo, a watanni ukun da suka wuce ba karamin matsala Samha take basa ba, kullum jarabanta karuwa yake abu kadan xata daga masa hankali da fitina, gashi bai son hayaniya duk ta sa ya rame, sai dai ynda take sllh bbu fashi ke burgesa yake kuma jin tausayinta tunda aikin baban giwa kawai take, kuma girman cikin bai hanata sllh ynda ya kamata ba, bata ma son kusantarsa ko kuma shi ya kusanci inda take bare ma ya dinga yin abubuwan da Anty tace yyi don jan hankalinta, fata yake ta sauke cikin nn lfya ya samu kwanciyar hankali, ta dawo Samha dinsa ta da mai miskilanci, shi dai yasan wasu masu ciki na da bala'i amma nata daban ne, yanxu kam cikin ya fito sosai sai kayi tunanin haihuwa yau ko gobe amma watannin cikin bakwai, har lkcn kuma bbu wani aikin da take don cikin yyi mata nauyi sai uban bacci kmr k'asa, hakan yasa yake tausayinta, babban tashin hankalinsa idan ranan Antenatal ya xagayo, da kyar da kyar yake lallabata su je asibiti, iyakar abinda take a gidan shine ta girka abinda xata ci me yawa kuma ita kadai ke cinye kayanta ko tayi bata masa, kuma ko sau daya bai damuwa da abinda take masa, sai ma dariya da ta ke basa, lkci lkci Abbanta na kiranta ta wayarsa har ma shi ma su gaisa, babban tashin hankalin da yafi na Antenatal a gun Abuturrab shi ne idan fatima ta xo gida weekend to fa ba shi da kwanciyar hankali har sai ta koma sch don wani shishshige masa take gaban ko waye har uwarta, Samha kuwa in ta dinga masa jaraba rike kai kawai yake don xuwa ynxu ciwon kai hayaniyarta ke sa masa, ynxu dai kwana biyu masifar ya lafa kuma ya rasa dalili, jin fitowarta daga daki ya dago yana kallonta, tayi masa kallo daya ta wuce kitchen, a hankali yace "Baby..." Juyowa tayi tana kallonsa yace "Kuna jin yunwa knn" dauke kai tayi ta shige kitchen ta daura shinkafa ta fito, parlon ta dawo ta xauna kan 2sitter, har hakan ya basa mamaki yau kuma ta xauna gu daya da shi, bayan minti bakwai ya juya ya ga ta kwanta ta rufe ido, kallonta ya dinga yi, can yyi murmushi ya mike ya wuce daki, jaka ya bude ya fiddo kayan xanensa da ke cikin jakar da Maminsa ta aiko masa da, ya fito parlor ya xauna inda yake yayi sharpen din pencil din snn ya dau takardan ya daura kan hannun kujeran ya fara xana ta, ya fi minti talatin yana xanen kafin ya mike ya dau stool ya dawo kusa da ita ya daura takardan ya duka ya ci gaba daga inda ya tsaya, bayan minti goma ta bude ido a hankali jin k'aurin shinkafa, ja baya yyi da sauri, ita ma kmr warce aka mintsila ta mike tana kallonsa tace "What r u doin here?" Kame kame ya fara ta karbe takardan a hannunsa tana kallo, kasa daina kallon xanen tayi, a hankalo yace "Am sorry Baby bari a yaga idan baki so..." Ta dago kai ta kallesa, murmushin da ya bayyana fararen hakoranta tayi underneath her breathe tace "Woaw i love it, it's perfect" Murmushin shi ma yyi don har ya mance rabon da tayi masa murmushi yace "Really?" A hankali Tace "Yeahhh.... Doctor u remember the dog u drew....." Ya wara ido yace "Yea my dog" kasa daina kallonta yyi tuna farko farkon haduwarsu, ita ma din tunanin da take kenan ta kasa cewa komai, ya dawo kusa da ita ya kamo hannunta murya can kasa yace "That moment..... When we were still strangers to each other, ranan da na fara daura idanuwana a kanki kina cewa in taimake ki, though u didn't think twice before leaving ganin cigarette a hannu na, how i saved u at the end, the day we met again at d front of my gate with my frnds, how u came back greeted and thanked me, how i was stunned seeing a Rosary round ur neck, ranan da na baki lift daga bakin titi, the day u gave me ur textbook to draw for you, a mammalian heart nd the Human Skeleton, the day u came into our compound nd was frightened by my big dog, how.... How i made you feel at home..... And that was how everything started.... " daga haka yyi murmushi yana kallon idonta da ya cicciko, rungumesa tayi, ya lumshe ido yace "I have always love u from the very beginning Samha" a hankali tace "Me too" kwace kanta tayi tace "My rice...." Daga haka ta mike da sauri tayi kitchen yace "Baby ki yi a hankali dnt harm ur self nd our babies" Ranan dai ya ci sa'a cokali biyu ta saka a shinkafa da mai da yajin da ta xubo a plate, ya lura she derives pleasure eating shinkafa da mai da yaji, bbu ynda ya iya shi da ba son yaji yake ba haka suka ci abincin, yamutse fuska ta fara yi bayan sun gama ci yace "Baki koshi ba ko baby?" Kamar xata yi kuka tace "It's kicking me" Ya d'an xaro ido don idan akwai abinda ta tsana baby yayi kick dinta ta dinga complain knn har da kuka wani lkcn, yace "Forgive dem plss, na sha gaya maki wasa fa suke maki dear, they are just being lively in der momy's womb....." A fusace tace "Don ba kai ake yi ma ba shi yasa xaka ce haka..." Tashi tayi da kyar ta nufi kofar fita ya bi ta da kallo yana murmushi, shi bai taba ganin mai jin haushi idan abun cikinta yyi motsi ba sai a kan Samha, Danna bell aka yi gabansa ya fadi, ya mike ya nufi kofar, fatima dai ce tsaye da kawayenta biyu, Samha dake xaune balconyn don in dai ta koshi nan take xama ta juya tana kallonsa, ya hade rai yana kallon fatima yace "Ya aka yi?" Wani kallo tayi masa ta hade rai ita ma tace "Ummi tace a karbo mata makullin motar ka nata na gun mechanic" Bai ce komai ba can ya juya ya koma ciki, wani tsaki Samha ta ja ta mike xata wuce ciki, ita dai fatima bata ce komai ba, Salima tace "To fah, da wa kuma matar gidan take, dake dai ko fatima?" fatima tayi dariya tace "Ke nifa kallo kafurai basu ishe ni ba wllh, da dai musulmai ne yan uwana....." Ae ko rufe baki bata yi ba Samha ta fincikota ta sauke mata tagwayen mari kan kace me sai gashi ta yi kasan balcony da ita ta shiga nakadar ta, Ihun da Salima tayi ya ja hankalin Abuturrab dake daki ya rasa ynda xai fito da makulli kar Samha ta cinyesa, xaro ido yyi ganin abinda Samha ke wa fatima, su Salima sun kasa ta6uka komai a tsaye, ya sauka kasan ya janye Samha a fusace yace "Kee, Are you stupid, kina hauka ne xa ki hau ta da duka? Kina ma da hankali kuwa yarinyar nn?" Saketa yyi ganin da yyi fatima numfashinta na seize, Samha ta juya ta shige gida ta bar su a gun, dagota yyi ganin xata samu attack yayi part dinsu da ita da sauri, Ummi dake parlor tana ta jiran makulli ta mike tace "Subhanallah, ya aka yi?" Ya xaunar da ita kan kujera, kan yace komai Ummi ta wuce ciki don dauko mata inhaler, su Salima suka shiigo parlon, Ummi na fitowa ta mika ma Abuturrab inhalern tana kallon su Salima tace "What happened?" Salima ta tabe baki tace "Matarsa ce ta hau ta da duka" Shiru Ummi tayi tana kallonsu, bata kuma cewa komai ba, Abuturrab kam bai iya dagowa ya kalleta ba har fatima ta dawo dai dai sai dai kuma da sauri take breathing, Ummi ta kalli su Salima tace "Ku shiga da ita bedroom" suna wucewa daki, Abuturrab ya dago da kyar yace "Mami don Allah kiyi hakuri, i don't knw whats...." Katse sa tayi tace "Noo ba komai boy, it's okay bani makullin" mikewa yyi duk jikinsa yyi sanyi ya mika mata makullin ya juya ya fita, Daki ya tadda Samha fuskar nan nata a murtuke, cikin fushi yace "Kinga you should be careful Samantha, matsalar ki ya fara isana, a kan wani dalili xa ki kama yar mutane da duka, are you mad?" Ta kallesa a takaice tace "I am not" daga haka ta mike xata fice dakin ya fixgota a mugun fusace yace "Kee, ni kike ce ma you are not??" Kkrin kwace kanta ta shiga yi tana huci tace "How will i admit i am mad, da ina hauka xan baka sha'awa har kaji kana so na, har ka rabo ni da iyayena, har ka aureni, let go of me right away Aliyu" a tsawace ta kare maganan, daga nan ta dinga masa tsawan ya saketa tana kokuwa da shi, ba karamin daurewa yyi ba na ganin bai wanka mata mari ba, ya dunkule hannunsa jin irin urge din da hannun ke basa na ya wanketa da mari, ganin idan ya ci gaba da saurarenta baxai iya controlling kansa ba ya turata har sai da ta buge da bango ya fice daga dakin kamar wani xaki, ficewa gidan yyi gaba daya, rabon da yaji irin wnn bacin ran har ya mance, wani xugi xuciyarsa ke masa, fuskar nn tasa bbu alamar rahama ya dinga tafiya down the street, can ya sa hannu aljihunsa ko akwai kudi ya fiddo dari biyar ya nufi gun wani me kiosk dake kofar wani gida, kwalin cigarette ya nuna ma mai kiosk din ya dauka ya mika masa, karba yyi ya mika masa kudin ya dau lighter da ya gani ya bar gun, gida ya koma ya shige bedroom dinsa ya sa key ya bude taban ya fara abinda ya dde bai yi ba, Samha kam dama yana fita taci kukanta me isanta tayi karfin halin tashi ta dauko yar jaka ta fara xuba kayayyakin ta ciki, Abuturrab na gama xuke xukensa bacci ya daukesa, bai yi minti goma yana baccin ba karan wayarsa ya tada sa, ya bude ido da kyar yana kallon wayar, can ya mike xaune ya jawo wayar, har lkcn bai ji xuciyarsa ta dawo masa dai dai ba duk da yaji sauki ba kamar daxu ba, hajiya Mariya ce ke kiransa ya daga wayar ya amsa sallamarta snn ya gaisheta, tace "Ya naji muryar ka haka Aliyu are you okay" yace "am okay mum bacci nayi" tace "Samha fa" yayi shirun kusan second biyar snn yace "She's fine mum" Hajiya Mariya tace "Hajiya Hajarah tace min cikinta ya tsufa koh?" Yace "Ehh" tayi shiru kafin tace "Are you okay kuwa Aliyu?" Yace "Mum daga bacci na tashi ne" tace "Toh shkkn, Aliyu ina tunatar da kai ka rike azkar da tsayuwar dare, kayi ta addu'a son, i had a dream that's nt encouraging...." A takaice yace "In shaa Allah mum" tace "Sai mun yi waya, Allah yyi albarka a gaida Samha" "Ameen" kadai yace ya katse wayar ya mike ya shiga bathroom, yana fitowa ya bude kofar dakin dai dai lkcn da Samha ta fito daga daki da jaka, wani kallo yayi mata daga sama har kasa, ita ko ko kallonsa bata yi ba xata wuce ya fixgota, sai da ta girgixa da irin fixgar da yyi mata, cikin kaushin murya yace "If am nt mistaken ai ba da kaya kika shigo gidan nan ba". Bata kallesa ba ta sake jakar hawaye na sakko mata tace "Naji toh" turata yyi har sai da ta kusa faduwa ta juya ta bar wajen, ta nufi kofar parlor ta fice daga gidan, tafiya take har ta isa bakin titi, ba karamin daurewa tayi na ganin ta tsaida hawayen dake xuba mata ba, ta tsayar da adai daita, a hankali tace "Don Allah ka taimake ni ka kai ni tasha ban da kudi" Hawaye na sakko mata ta kare maganan, yace "Ba can nayi ba," daga haka ya ja adai daitansa, ta tsayar da adaidaita yafi biyar kafin ta samu wani bawan Allah da yace ta shiga, haka ya kai ta tashan tayi masa godiya snn ta wuce ciki, direct gun motar kano ta nufa, nan tayi ta tsayuwa ta rasa abin cewa tun ana tambayarta inda xata har aka kyaleta, wata Hajiya ce aka sauke a mota ta nufeta da sauri, tana kkrin mayar da hawayen idonta tace "Mumy don Allah ki taimaka ki biya min kudin mota bani da kudi" kallonta kawai dattijuwar ke yi, sai taji tausayinta a tunaninta yawon duniya ta fito yi, ta kalli uban cikin dake gabanta ta girgixa kai tace "Toh shiga" risinawa tayi tayi mata godiya snn ta shiga motar, matar ma ta shiga ta bada kudinsu, nn da nn motar ya cika suka dau hanyar kano. *Haske writers asso* [11/30, 7:16 AM] ‪+234 814 219 6835‬: 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 83..... Har suka yi nisa Samha bata daina hawayen da take cikin motar ba, bbu wanda yasan abinda take don ta rufe fuskarta da hijab din jikinta, lkci lkci Hajiyan kan kalleta don tana gabanta ne, gajiya tayi da kukan ga wani yunwa da take ji, can bacci ya dauketa, sai kusan shidda suka isa kano, matar da ke gefenta ne ta tada ta don har an fara sauka a motar, ta bude ido da kyar ita ma ta fito daga motar ta tsaya tana kare ma park din kallo, can ta hango matar da ta biya mata kudin mota suka hada ido don kallonta matar take, a sanyaye ta karasa kusa da ita kanta a kasa tace "Mumy na gode, Allah ya saka da alkhairi" Hajiyar tace "Ameen, ya sunan ki yarinya?" Ta kalleta a hankali tace "Sunana Samha" Hajiyar tace "Kin taba xuwa kano kuwa Samha" Gyada mata kai Samha tayi, matar tace "Toh wani anguwa xa ki?" Wasu sabbin hawaye ne suka taru idonta, matar tace "Ina mijin ki?" Share hawayen tayi nan ma bata ce komai ba, wani bakin ciki yasa ta fashe da kuka sosai, matar tace "Subhanallah, ni bnce kiyi kuka ba Samha, ki fadi inda xa ki, xa a xo daukata sai in rage maki hanya ko kuma in baki kudin adai daita ki wuce" Matar bata kuma cewa komai ba ganin Samha ta ki bata amsa, ko minti biyar basu kara a tsaye ba wani mota ya shigo park din, dai dai inda Hajiyar ke tsaye motar ya tsaya, wani mutum da baxai wuce shekara 40 ba ya fito ya isa har inda take da fara'a yace "Sannu da isowa Umma, ya hanya" tace "Alhmdllh Ahmad...." daga haka ya bude mata back seat ta kalli Samha tace "Shiga...." sai a snn mutumin ya kalleta yace "Ohh bn kula tare ku ke ba, sannun ku da isowa" gaishesa Samha tayi ya amsa da fara'a yace ta shiga, sai da ta shiga motar snn Hajiya ta shiga ya rufe ya shiga maxaunin driver, tun da suka shiga motar Hajiyar ke ta hira da d'an nata, jin Samha bata ce xata sauka a ko ina ba yasa bata yi mata magana ba har suka iso gidansu dake Shagari qtrs, mutumin yyi horn gaban gate din wani babban gida mai gadi ya bude gate din, yana parking a space da aka tanadar don haka ya fito ya bude mahaifiyarsa ta fito snn Samha ma ta fito, wasu yan mata ne har su uku suka fito a daya daga part uku dake cikin babban compound din, can sai ga wata ma ta fito daga wani part din da yara uku, duk suka taho da murna gun matar, sai bayan da suka gaisheta snn matar da ta fito da yara uku ta kalli Samha tace "Sannun ku da xuwa, ya hanya" Samha ta kirkiri murmushi tace "Alhmdllh" sauran yan matan ma duk suka gaisheta da fara'a daga haka Umma tace su shiga ciki kafin a kira Magrib, babban parlor ne sosai duk suka xaxxauna Umma na kallon yar ta Farida tace "Farida ku shiga da ita ciki ta huta" Farida ta mike tana kallon Samha tace "Mu je Anty" mikewa Samha tayi ta bi bayanta suna shiga wani daki farida ta nuna mata gado tace "Xauna sai in hada maki ruwan wanka" daga haka ta shiga bathroom, ba a dau lkci ba ta fito ta ciro xani a Press dinsu ta mika ma Samha tace "Ki shiga" Samha ta karba a hankali tace "Na gode" daga haka ta shiga bayin, ko da ta fito har an kawo mata abinci, Sumayya ta dauko mata doguwar rigarta ta ajiye mata da man shafawa tace "Ga kaya nn" Samha tace "Toh nagode, xan yi sllh" Darduma yarinyar ta shimfida mata ta fita, la'asar tayi snn magrib don har an kira, tana xaune kan darduma mata me yara uku wanda da alama wanda ya dauko su a park ne mijinta ta shigo dakin da warmer tace "Sannu bakuwa" murmushi Samha ta kirkira ta kasa cewa komai, matar me suna Maryam ta ajiye warmern tace "Ki ci ynxu kar ya huce" Cikin sanyin murya Samha tayi mata godiya, Maryam ta fita, Sadiya ce ta shigo dakin, ita ma dai 'ya ce ga Umma ta gaida Samha tayi mata ya hanya snn ta fita, da kyar Samha ta mike ta shiga shiryawa, haka kawai hawaye ke xubar mata ta rasa dalili, ta gama sa kayan ta xauna kasa ta jinginar da kanta da gado, Sumayya ta shigo dakin tace "Baki xuba abincin ba Anty" durkusasawa tayi ta bude abincin ta shiga dibar mata, tana diba ta kai mata gabanta, ta dauko pepper soup din da Maryam matar yayanta ta kawo mata shi ma ta ajiye gabanta, Samha ta d'an yi murmushi tace "Baki gaya min sunanki ba" tace "Sunana Sumayya" Samha tace "Nagode Sumayya, ni sunana Samha" murmushi Sumayya tayi tace "Haba dai, welcm to our home samha" daga haka ta mike ta fita daga dakin, ba laifi Samha ta ci abincin sbda yunwar da take ji, da taji ta koshi ta kwantar da kanta jikin gado ta rufe ido, Sadiya ta shigo tace mata ta hau gado mana, mikewa tayi ta hau kan gadon. Tun da Samha ta bar gida Abuturrab ke kwance idonsa a lumshe, shi dai ba bacci yake ba ba komai ba, sai kusan karfe biyar a lkcn ya mike xaune, rike kansa da yyi masa nauyi yyi, ga wani ciwo da kan ke masa, ragowar tabarsa ya dauko ya xari daya ya kunna ya kai baki, me yasa yarinyar nn ke neman sa masa hawan jini da ciwon xuciya ne, can dai yyi karfin halin mikewa tsaye ya kashe sauran taban ya jefar ya fita daga dakin, duk da yasan bata dakin nata hakan bai hanasa tura kofa a hankali ba, he just don't want to believe da gaske barin gidan tayi, bbu kowa dakin as he already know, ya juya da kyar ya wuce parlor, nn ma tsaye yyi na kusan minti goma kmr yana jiran ganin billowanta, can ya nufi kitchen nn ma ya gama tsayuwarsa ya dawo parlorn ya xauna ya rike kai, kmr wanda aka tsikara ya mike da sauri yace "Noo" dakinsa ya koma xai dauka makullin mota sai ya tuna ae ya kai ma Ummi, fitowa yyi ya bar parlon ya fita compound, tafiya kawai yake amma wani juya masa kansa ke yi, ya nemi dakali ya xauna ya rike kan, ta ina xae xai fara nemanta, ita dai ba da kudi ta bar gidan ba, ba kuma kawaye gareta a garin ba, infact bata ma san kowa ba, tunanin hakan yasa shi mikewa da sauri, lkci daya hankalinsa ya tashi, to ina xata je haka, tafiya ya dinga yi har ya isa bakin titi, ganin he is just lost ya ciro wayarsa a aljihu ya shigw kiran Dr Shariff. Karfe goma da wani abu Sumayya ta shigo daki, ganin idon Samha biyu tace "Anty wai ki je in ji Umma" mikewa Samha tayi tace "Toh" Sumayya ta dauko mata hijab ta bata ta sa daga haka suka fita, Umma na bedroom dinta da yaranta maxa biyu Samha ta shigo da Sumayya, duk da manya ne su ma hakan bai hanasu gaida ta ba suka fita, Sumayya ma ta fita, Umma ta nuna mata gefen gado ta xauna, ta xauna kanta a kasa, Umma tace "Samha xan maki tambaya, but what i hate in my life is lying, kar ki min karya, kar kuma ki ji komai ki bn amsan tambayar da xan maki" Samha ta kasa dago kanta cikin sanyin murya tace "Toh" Umma tace "Kina da miji?" Kasa cewa komai Samha tayi sai hawaye, Umma tace "Nace kar ki ji komai ki min magana" fashewa da kuka tayi, Umma bata hanata ba tayi mai isarta tayi shiru, Umma tace "Answer me now" cikin sarkewar murya tace "Ina da shi Mumy" Umma tace "Na fa ce maki ban da karya" ta dago hawaye na sakko mata cikin sanyin murya tace "Ba karya nake ba Mumy" Umma tace "Toh yana ina?" A hankali tace "Gombe" Umma tace "Toh me ya faru kika bar gida?" Tana share hawayenta tace "Bana son sa kuma, ina son komawa gun iyayena" umma tace "Baki son sa? Yayi maki wani abun ne, kuma ko kin koma gun iyayen naki su ma ba barin ki xa su yi ba, ki kalli condition din ki fa, ki gaya min gskyan me ya sa kika baro gidan" tace "Mum idan na koma gun parent dina they will be happy that i am back duk da nasan i failed them...." Ta fashe da kuka sosai tace "Mum i wish i can start my life all over again, though m nt regretting coz everything happen for my good, but i wish ba ta wnn hanyar Allah ya nuna min *Noorul Huda* ba" Umma ta dafa shoulder dinta da tausayi tace "Kar ki yi Sa6o Samha, kuma nace kar ki min karya kuma kin min, baki da aure knn koh?" Ta rufe kanta jikinta tana kuka sosai tace "Allah ina da aure Mum, but i got married with out d knowledge of my parent, i chose a man over dem, a muslim for that matter" dagota Umma tayi da mamaki tana kallonta, Tana girgixa kai tace "I was born nd brought up in a Christian home, my name is Samantha...." Kallon Mamaki Umma ke mata ta rasa abun cewa, a hankali Samha ta ci gaba tace "I chose Aliyu a muslim over my parent...." Nan da nn jikin Umma yyi sanyi sosai, ynxu fa sai tace Aliyun yaudaranta yyi, kila ma tace sakinta yyi, nan da nan ranta ya baci ba kadan ba, me yasa xai 6ata ma islam suna haka, me yasa xai ci amana yyi betraying trust dinta yana matsayin musulmi, Samha ta sunkuyar da kai hawaye kam yaki tsaya mata, Umma ta riko hannayenta a hankali tace "Tell me about everything daughter.... Islam is nt d way you r thinking right now, share ur story with me" Samha ta gyada mata kai har lkcn hawaye na xuba idonta, a hankli ta soma bata labarin farkon haduwarsu da Aliyu.Umma sai kallonta take tana saurarenta with much interest, Samha bata dakata ba sai da ta kai har karshe, ta fashe da kuka sosai tace "Mum kinga ya min gorin ni na biyosa ae, ya kuma min gorin bn je gidansa da komai ba, ae wnn ba halin musulmai bane...." Rufe bakinta Umma tayi cike da tausayinta tana girgixa kai tace "You don't say anything about Aliyu now, but all this while me yasa ki ka ki karban islam gashi kina sllh, let this nt make you have doubt for islam Samha, rayuwar Antyn ki Maryam bai baki sha'awa, is der anything in islam that's nt good bayan ki cire abinda Aliyu yyi maki, kinsan a ko wani addini akwai dakikai...." A hankali Samha tace "Mum xan karba islam amma ba don na taba auren musulmi ba, xan karbi islam ba don Antyna ba ko kakana, sai don Allah, da abubuwa da dama da musulmai suka min, na shiga hannun musulmai da dama Mum, ban san ynda xan fadi maki kirkinsu da karramci ba which ba kowa ke haka ba a addinin iyayena don basu yrda da kansu ba balle wani, Mum tun daga kan Aunt din Aliyu... duk da addininmu ya sha bambam iyakar son da xata ma d'an da ta haifa ta nuna min, tana daya daga jerin mutanen da baxan mance ba a rayuwata, ban taba ganin mahaifiyarsa ba amma indai suka yi waya ita ma takan ce ya bani mu gaisa duk da rabata da d'an ta da nayi hakan bai sa ta ji haushi na ba, mum mun xauna a rigar fulani da muka bar kano, the muslims we met der where more than kind, sun yi accommodating dinmu ba tare da sanin daga inda muka fito ba ko inda xa mu, basu san xuciyar mu ba amma a haka suka xauna da mu which ba lallai d'an uwana Christian yyi min haka ba, muka je gombe.... Ummi ta min abinda ko wacce ta haifeni sai haka, ta rike ni kmr yar ta, bata taba kyamatata ba a matsayin wacce ba musulma ba, i knw i can never forget her too, haka ma yarinyar ta khadija, fatima kuma nasan mijina take so shi yasa take min abinda take yi, gun ta da sisters din Aliyu kadai na samu matsala su ma kuma ban ga laifinsu ba don if i where to be in der shoes iyakar abinda xan yi knn don na raba jini ba abun wasa bane, a zaria ma na xauna da musulmai da basu san ni ba ban san su ba su ma kuma sun min karamci ba kadan ba, Sai gashi na hadu da ke yau mum, baki san ni ba baki taba ganina ba kika taimakeni tun a tasha, bai tsaya iya nn ba har sai da kika kawo ni gidanki baki damu da ki fara bincike kafin ki yrda in shiga gidan ki ba, sai gashi gaba daya yaranki basu san ni ba, amma suka dauke ni kamar yar uwa duk a rana daya cikin kankanin lkci, dubi ynda kika xauna kina saurarata da xuciya daya baki yi tunanin ko karya nake maki ba kin kuma yarda dari bisa dari, Mum with this i knw islam rahama ne, musulmai daban suke a duk inda suke.... Kuma duk inda na xauna bbu wanda ya taba tilasta ni inyi addininsa ko da wasa, har shi kansa Aliyun, wanda da Christian home ne da tuni an fara fita da ni church, i wil be very proud to be among you, amma ni baxan komawa gun Aliyu ba, i prefer going back to my parent in ma kasheni ne su yi, but na bar Christianity da dadewa a xuciyata, na kuma dade da fadin La'ila ha illallah....." hawaye take sosai ta kai karshe, Umma ta jawota jikinta tana murmushi ita ma idonta ya kada sosai tace "Am happy for you Samha, amma ki yafe ma Aliyu, kinsan duk d'an adam ajizi ne...." Girgixa kai tayi tace "Na yafe masa Mum, ae ya min abinda baxan manta ba amma ni na hakura bana auren kuma, kilan rabon inyi converting ne Allah ya hada mu, don naji har cikin raina bna sonsa kuma, ba kuma yau na fara jin haka ba, for the past 3month nake jin hakan...." Umma tayi shiru kafin tace "Toh dama kana kishin abinda baka so" murmushi Samha tayi tace "Mum da gaske bna son sa yanxu, bna ma son in gansa" *Haske writers asso* can ta matse maki😜😂 Samantha [11/30, 7:59 PM] ‪+234 806 632 7659‬: 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 84..... Rudewa Mami tayi ganin aman jini yake tayi k'asa da shi ta dinga kiransa tana jijjigasa cikin tashin hankali, Abba tsaye yyi yana kallonsa da mamaki ya kasa cewa komai, Ramla da Ilham suka sakko jin muryar Mami, wani ihu suka saki a tare, Ramla ta taho da gudu ta durkusa ta rikesa ita ma cikin kuka tace "Ya Turab, Mami me ya same sa, dubi aman jini yake fah" juyawa Abba yyi ya koma parlor ya dau waya ya shiga kiran doctor dinsa. A yau litinin Samha ta xamo daya daga cikinmu bayan an yi duk abinda musulunci ya tanadar kafin yin hakan, wato dai ta amshi kalmar shahada, yanda Umma tayi farin ciki a wannan rana sai ka rantse ta hada abu da ita ne, shi kansa mai gidan ta Alhaji Ibrahim da abokansa biyu sai yaransa maxa gaba daya sun yi farin ciki da lamarin suka kuma yi mata fatan alkhairi suka kuma yi mata addu'ar Allah yasa ta dauwama a islam, shawarwarin da ya kamata suka bata suka kuma yi mata nuni da sai ta kauda kai a duk abinda xata gani gun yan uwanta nan gaba, sauran kuma suka bar ma Hajiya Halima, nan ita ma ta bata nata shawarar, sun jima sosai a parlon da umma bayan barin su maigidanta, ita dai Samha na xaune kanta a kasa, har lkcn ta rasa dalilin kukan da take, Umma tace "Bana son kukan nan daughter, ain't you happy?" Tana share hawayenta a hankali tace "I am" Umma tace "Good, kar ki sake xubda hawayenki, Allahu na tare da ke, kuma shine gatan ki xai kuma ji6anci duk al'amuran ki" kai Samha ta gyada mata, Umma tace "Kina da sunan da kike son a dinga kiran ki da shi ne?" Kallonta Samha tayi sai kuma ta girgixa kai, Umma tayi murmushi tace "Alryt we will call you *Noor* meaning *Light* kina so?" Murmushi Samha tayi a hankali tace "Toh Umma" tace "Kina xuwa Antenatal ne a can gombe?" Kai ta gyada mata ba tare da ta dago ba, Umma tace "Alryt, tafi ki je ki huta, koh gobe sai Maryam ta raka ki asibiti" Mikewa tayi tace "Nagode Mum" daga haka ta wuce daki, a bedroom Umma ta xaunar da yaranta gaba daya da surkanta biyu ta fadi masu matsayin Samha ta kuma basu takaitattacen labarin da Samha ta bata jiya, duk sun ji tausayinta sosai, nan Umma tace "Ke Sumayya tunda kina gida always sai ki dinga lura da ita kina putting din ta through, tun daga kan alwalarta da sallah, kiyi kkrin dinga nuna mata do's nd don't's din islam, snn kiyi kkrin dinga koya mata addu'o'i, har ma da karatun qur'an, i notice she's not totally an illiterate in islam, kema sai ki samu lada gun Allah in kika yi xuciyar ki daya" Sumayya tace "Toh Umma" Umma ta kalli Maryam da Rukayya tace "Ku kuma ta fannin auratayya nake son kuyi putting dinta through" su ma suka amsa, nan tace ma 'ya yan nata duk Noor xa su dinga kiranta da. A hankali Abuturrab ya bude idonsa ya saukar saman dakin, sosai yake jin nauyin idanuwan nasa, kare ma inda yake kwance kallo ya shiga yi a hankali yaga bedroom din kamar na Abbansa, idonsa ya sauka kan alluran dake vein dinsa, kallon ledan ruwan yyi lkci daya ya mike xaune xai tuge yaji muryar Abbansa, "Don't you try that!" Juyawa yyi da sauri suka hada ido, lkci daya abubuwa suka dinga dawo masa, rike kansa yyi jin wani tukukin da xuciyarsa ke yi yace "Nooo" Abba ya karaso da sauri yyi gripping shoulders dinsa yace "Are you okay" ya daura kansa jikin Abbansa cikin rawan murya yace "She's gone Abba...." Mami ce ta shigo dakin tare da Hajiya Mariya jin muryarsa, Hajiya Mariya ta karasa da sauri ta dago sa tace "Aliyu...." Bude ido yyi yana ganinta ya rungumeta cikin raunin murya yace "Mum don Allah don annabi kice mata ta dawo" da damuwa Hajiya Mariya tace "Then ka nutsu tukun son, ba fa inda ta je tana gida dama...." Saketa yyi da sauri yace "Da gaske Mum" bai jira cewarta ba ya yunkura xai mike tsaye tana kkrin mayar da shi amma tuni ya tashi, wani mugun bugu xuciyarsa yyi, ya dafa gun da hannu biyu, Mami ta rude tace "Innalillahi, Col ka kira likitan don Allah" tare suka yi kasa da Hajiya Mariya don kasa tsaye yyi, Strictly Abba yace "If anything shud happen to my son..... Wllh duk sai kunyi mamaki na, i will make sure you two pay for this, yanda ku ka munafurce ni ku ka boyesa da yarinyar for all this while haka xaku nemota ku kawo masa ita ynzu idan ba haka ba......" A tsawace yace "kowa ma sai ciwon xuciya ya kamasa" Wani harara Mariya ta watsa masa ta gefen ido a fusace tace "Don Allah mu wuce asibiti yaya, ki kira masu gadi su taimaka mana a sa shi a mota" fita Mami tayi tana hawaye taje kiran soldiers din waje. Suna xaune a ward din da aka basu su kadai, Ramlah na xaune kusa da shi sai hawaye take haka ma Khaleesat, Ilham kam na gefen Mami ita ma kukan take, Mami dai ta xuba uban tagumi idonta a kansa ganin mugun ramar da yyi, bacci yake amma da gani kasan na dole ne, hawaye ne ya xubo idonta jin abinda likitocin suka gaya mata, Aliyunta da ciwon xuciya kuma, wnn wace irin kaddara ce, sallamar Hajiya Mariya da Ummi ne ya katse mata tunaninta, suka shigo ward din Shariff na biye da su a baya, Mami ta d'an yi murmushi tace "Sannu da isowa Hajiya" Ummi dake ta kallon Aliyu ta karaso a sanyaye bakin gadon ta tsaya ta daura hannu forehead dinsa, Shariff ma tsaye yyi yana kallonsa, Mami tayi karfin halin cewa "Ina yinin mu Hajiya" Ummi ta kalleta, sai ta ji tausayinta har cikin ranta, ta kasa amsa gaisuwar, kujera ta samu ta xauna, ta rike kai, can ta dago ta kalli Hajiya Mariya dake tsaye ita ma, tace "Hajiya ina gidan iyayen yarinyar yake kika ce?" Hajiya Mariya tace "Anguwarsu daya da yaya ai" Tace "Toh ko mu je can" Ita dai Mami bata ce komai ba, Ummi ta tuna ai sun yi exchanging number da Anty Maryam, tace "Ai ina ma da number Aunt dinta ta kaduna, musulma ce ita, bari a kira ko can tayi" daga haka ta shiga kiran Anty Maryam, tana dagawa bayan sun gaisa Ummi ta rasa ynda xata yi tambayar, can dai tace "Maryam, tambayarki xanyi don Allah ko Samha taje gun ki?" Anty Maryam dake xaune sai da ta mike tsaye tace "Wajena kuma?" Ummi tace "Tun jiya ba mu ganta ba Maryam" Salati Anty Maryam ta saki tace "Ba a ganta ba kuma Hajiya??? nima ba ta xo nan ba wllh, meke faruwa ne" rasa abun cewa Ummi tayi can dai ta katse wayar. Da yamma Abba da kansa ya tafi gidansu Samha, mai gadi ya kira masa Abban samha don yana gida shima, lkci daya Abban Samha ya ganesa, suka gaisa, Abba yace "Dafatan ka gane ni...." Abban Samha yace "Kwarai kuwa" Abba yace "Maa sha Allah, magana nake son muyi ta fahimta Mr???" Abban Samha yace "David." Abba yace "Alryt Mr David, yar ka ta dawo gida koh" kallonsa kawai Mr David ke yi, can yace "I don't get the question" Abba yace "I want to know if ur daughter is back home" Mr David yace "Noo, amma ai xa ku fi mu sanin ko ta dawo ko bata dawo ba, ba d'an ka ne ya tafi da ita ba, kuma ya aureta" Muryar Mahaifiyar Samha suka ji a kansu tana ma kallon Col sama.da kasa tace "Ehen, Oga Soldier how may we help you kun dawo min da yarinya ta ne ko yaya?" Mikewa Col yyi yace "Ae yar taku bata gun d'a na kuma, shine na xo to find out ko ta dawo maku ne...." Daga haka ya mike yace "I leave you both in peace" da gudu tace "Ban gane basa tare ba malam..." Col ya juyo ya kalleta yace "Ba sai kin gane ba, but just know that my boy is back alone" daga nan bai kuma saurarenta ba ya fice, ta dinga juya maganan a kai wai his son is back, toh ita samanthan fah, kallon Mr David tayi kafin ta wuce ciki da sauri, shi kam komawa yyi ya xauna ya dau wayarsa ya shiga kiran layin Abuturrab, amma har ya katse ba a dauka ba, Rachael ta fito da dankwali daure kanta ba tare da tace ma mai gidan nata komai ba ta nufi gate, gidansu Abuturrab ta wuce, dai dai lkcn da Ummi da Hajiya Mariya suka iso gidan, kallon Ummi tayi tace "Kin ga mahaifiyar yarinyar can" Ummi dake ta kallon Rachael dake tsaye soldiers din bakin gate basu bar ta ta shiga ba, Hajiya Mariya ta fito sannan Ummi suka nufi gate din, Rachael na ganin Hajiya Mariya tace "Yauwa ji nayi wai tantirin d'an ku ya dawo ashe, to ina ya baro min 'ya ta?" Hajiya Mariya tace "Ehh toh, xa mu iya komawa asibiti ki tambayesa" Ta hade gira tace "In je asibiti in tambayesa kuma, asibiti ya koma rayuwa?" Hajiya Mariya tace "Kwarai" Ummi dai sai kallon Rachael take, Rachael tace "Toh ae sai mu je, don wnn karan idan na yrda shegiya nake, ba soldier ba, idan ma mala'ika ne ubansa ba yrda xan ba" Ummi tace "Subhanallah, Madam bai kai ga haka ba" A tsawa ce Rachael tace "To God who made me ya kai haka" Daga nan ta nufi mota fuu, Hajiya Mariya ta kalli Ummi tace "Hajiya mu je kawai" Daga haka suka bi ta, Tana biye da su a baya bayan sun isa asibitin fuskar nan nata a murtuke har suka iso ward din da Abuturrab yake, Shariff ne ke ta kwantar masa da hankali, shi kam ya jingina da bango idonsa lumshe har lkcn xuciyarsa bai bar xugin da yake ba, wani lkcn kuma yaji gabansa yyi mugun faduwa, Maganganun Ummi ne yyi tasiri kansa har ya d'an samu nutsuwa amma ya kasa cewa komai har sannan, Mami kuma na xaune kusa da shi tare da su Ramla dake kallonsa cike da tausayi, Rachael na fadowa ward din ta nufesa tana kare ma ruwan dake hannunsa kallo tace "Where is my daughter???" Bude ido yyi yana kallonta bai iya yace komai ba, ta iso gabansa sosai, a fusace tace "Nace ina 'ya ta" lkci daya idanuwansa suka kada a hankali ya dinga kai hannunsa kirjinsa, Dr Shariff ya mike yace "Madam don Allah ki bar nan, ba ki ganin condition dinsa ne....." Tsawa tayi masa tace "Bbu inda xanje ya fito min da Samantha, ya xa ayi ya dawo shi kadai batun ba shi kadai ya tafi ba, ina ya baro min 'ya ta kashe min ita yyi ko sayar da ita" tana kai wa nan ta fashe da kuka sosai tana tafa hannu tace "Ohh jesus what have i done to deserve this, gashi ya dawo bbu 'ya ta, kila ma ya kasheta ne, kila mutuwa tayi" tana kai wa nn Abuturrab ya tuge alluran hannunsa ya sakko daga kan gadon xai fita dakin, Shariff ya rikosa, wani kara da ya tsorata Rachael yyi ya tura Shariff xai fita da sauri Ummi ta rikosa tace "Are you on ur right senses Aliyu, baka da hankali ne, baka ga halin da kke ciki ba, ina xaka??" Tun jiya sai a lkcn hawaye ya shiga sakko masa ya rungumeta cikin raunin Murya yace "Mami ban san halin da take ciki ba, ban san inda ta tafi ba, you know her condition Mami, i can't take this any longer ji nake kamar xuciyata xata buga, it's hurting me" jansa tayi ta xaunar da shi kan kujera cike da tausayinsa take "Na fa ce xa a ganta boy, kai ba musulmi bane, me yasa baxa ka sa dangana a xuciyarka ba, in shaa Allah duk inda take tana lafiya kuma xata dawo gare mu" Rachael dai sai kallonsu take uwa idanuwan nn xa su yi magana, can dai ta fice bata xame ko ina ba sai gun Priest. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 85..... Rudewa Mami tayi ganin aman jini yake tayi k'asa da shi ta dinga kiransa tana jijjigasa cikin tashin hankali, Abba tsaye yyi yana kallonsa da mamaki ya kasa cewa komai, Ramla da Ilham suka sakko jin muryar Mami, wani ihu suka saki a tare, Ramla ta taho da gudu ta durkusa ta rikesa ita ma cikin kuka tace "Ya Turab, Mami me ya same sa, dubi aman jini yake fah" juyawa Abba yyi ya koma parlor ya dau waya ya shiga kiran doctor dinsa. A yau litinin Samha ta xamo daya daga cikinmu bayan an yi duk abinda musulunci ya tanadar kafin yin hakan, wato dai ta amshi kalmar shahada, yanda Umma tayi farin ciki a wannan rana sai ka rantse ta hada abu da ita ne, shi kansa mai gidan ta Alhaji Ibrahim da abokansa biyu sai yaransa maxa gaba daya sun yi farin ciki da lamarin suka kuma yi mata fatan alkhairi suka kuma yi mata addu'ar Allah yasa ta dauwama a islam, shawarwarin da ya kamata suka bata suka kuma yi mata nuni da sai ta kauda kai a duk abinda xata gani gun yan uwanta nan gaba, sauran kuma suka bar ma Hajiya Halima, nan ita ma ta bata nata shawarar, sun jima sosai a parlon da umma bayan barin su maigidanta, ita dai Samha na xaune kanta a kasa, har lkcn ta rasa dalilin kukan da take, Umma tace "Bana son kukan nan daughter, ain't you happy?" Tana share hawayenta a hankali tace "I am" Umma tace "Good, kar ki sake xubda hawayenki, Allahu na tare da ke, kuma shine gatan ki xai kuma ji6anci duk al'amuran ki" kai Samha ta gyada mata, Umma tace "Kina da sunan da kike son a dinga kiran ki da shi ne?" Kallonta Samha tayi sai kuma ta girgixa kai, Umma tayi murmushi tace "Alryt we will call you *Noor* meaning *Light* kina so?" Murmushi Samha tayi a hankali tace "Toh Umma" tace "Kina xuwa Antenatal ne a can gombe?" Kai ta gyada mata ba tare da ta dago ba, Umma tace "Alryt, tafi ki je ki huta, koh gobe sai Maryam ta raka ki asibiti" Mikewa tayi tace "Nagode Mum" daga haka ta wuce daki, a bedroom Umma ta xaunar da yaranta gaba daya da surkanta biyu ta fadi masu matsayin Samha ta kuma basu takaitattacen labarin da Samha ta bata jiya, duk sun ji tausayinta sosai, nan Umma tace "Ke Sumayya tunda kina gida always sai ki dinga lura da ita kina putting din ta through, tun daga kan alwalarta da sallah, kiyi kkrin dinga nuna mata do's nd don't's din islam, snn kiyi kkrin dinga koya mata addu'o'i, har ma da karatun qur'an, i notice she's not totally an illiterate in islam, kema sai ki samu lada gun Allah in kika yi xuciyar ki daya" Sumayya tace "Toh Umma" Umma ta kalli Maryam da Rukayya tace "Ku kuma ta fannin auratayya nake son kuyi putting dinta through" su ma suka amsa, nan tace ma 'ya yan nata duk Noor xa su dinga kiranta da. A hankali Abuturrab ya bude idonsa ya saukar saman dakin, sosai yake jin nauyin idanuwan nasa, kare ma inda yake kwance kallo ya shiga yi a hankali yaga bedroom din kamar na Abbansa, idonsa ya sauka kan alluran dake vein dinsa, kallon ledan ruwan yyi lkci daya ya mike xaune xai tuge yaji muryar Abbansa, "Don't you try that!" Juyawa yyi da sauri suka hada ido, lkci daya abubuwa suka dinga dawo masa, rike kansa yyi jin wani tukukin da xuciyarsa ke yi yace "Nooo" Abba ya karaso da sauri yyi gripping shoulders dinsa yace "Are you okay" ya daura kansa jikin Abbansa cikin rawan murya yace "She's gone Abba...." Mami ce ta shigo dakin tare da Hajiya Mariya jin muryarsa, Hajiya Mariya ta karasa da sauri ta dago sa tace "Aliyu...." Bude ido yyi yana ganinta ya rungumeta cikin raunin murya yace "Mum don Allah don annabi kice mata ta dawo" da damuwa Hajiya Mariya tace "Then ka nutsu tukun son, ba fa inda ta je tana gida dama...." Saketa yyi da sauri yace "Da gaske Mum" bai jira cewarta ba ya yunkura xai mike tsaye tana kkrin mayar da shi amma tuni ya tashi, wani mugun bugu xuciyarsa yyi, ya dafa gun da hannu biyu, Mami ta rude tace "Innalillahi, Col ka kira likitan don Allah" tare suka yi kasa da Hajiya Mariya don kasa tsaye yyi, Strictly Abba yace "If anything shud happen to my son..... Wllh duk sai kunyi mamaki na, i will make sure you two pay for this, yanda ku ka munafurce ni ku ka boyesa da yarinyar for all this while haka xaku nemota ku kawo masa ita ynzu idan ba haka ba......" A tsawace yace "kowa ma sai ciwon xuciya ya kamasa" Wani harara Mariya ta watsa masa ta gefen ido a fusace tace "Don Allah mu wuce asibiti yaya, ki kira masu gadi su taimaka mana a sa shi a mota" fita Mami tayi tana hawaye taje kiran soldiers din waje. Suna xaune a ward din da aka basu su kadai, Ramlah na xaune kusa da shi sai hawaye take haka ma Khaleesat, Ilham kam na gefen Mami ita ma kukan take, Mami dai ta xuba uban tagumi idonta a kansa ganin mugun ramar da yyi, bacci yake amma da gani kasan na dole ne, hawaye ne ya xubo idonta jin abinda likitocin suka gaya mata, Aliyunta da ciwon xuciya kuma, wnn wace irin kaddara ce, sallamar Hajiya Mariya da Ummi ne ya katse mata tunaninta, suka shigo ward din Shariff na biye da su a baya, Mami ta d'an yi murmushi tace "Sannu da isowa Hajiya" Ummi dake ta kallon Aliyu ta karaso a sanyaye bakin gadon ta tsaya ta daura hannu forehead dinsa, Shariff ma tsaye yyi yana kallonsa, Mami tayi karfin halin cewa "Ina yinin mu Hajiya" Ummi ta kalleta, sai ta ji tausayinta har cikin ranta, ta kasa amsa gaisuwar, kujera ta samu ta xauna, ta rike kai, can ta dago ta kalli Hajiya Mariya dake tsaye ita ma, tace "Hajiya ina gidan iyayen yarinyar yake kika ce?" Hajiya Mariya tace "Anguwarsu daya da yaya ai" Tace "Toh ko mu je can" Ita dai Mami bata ce komai ba, Ummi ta tuna ai sun yi exchanging number da Anty Maryam, tace "Ai ina ma da number Aunt dinta ta kaduna, musulma ce ita, bari a kira ko can tayi" daga haka ta shiga kiran Anty Maryam, tana dagawa bayan sun gaisa Ummi ta rasa ynda xata yi tambayar, can dai tace "Maryam, tambayarki xanyi don Allah ko Samha taje gun ki?" Anty Maryam dake xaune sai da ta mike tsaye tace "Wajena kuma?" Ummi tace "Tun jiya ba mu ganta ba Maryam" Salati Anty Maryam ta saki tace "Ba a ganta ba kuma Hajiya??? nima ba ta xo nan ba wllh, meke faruwa ne" rasa abun cewa Ummi tayi can dai ta katse wayar. Da yamma Abba da kansa ya tafi gidansu Samha, mai gadi ya kira masa Abban samha don yana gida shima, lkci daya Abban Samha ya ganesa, suka gaisa, Abba yace "Dafatan ka gane ni...." Abban Samha yace "Kwarai kuwa" Abba yace "Maa sha Allah, magana nake son muyi ta fahimta Mr???" Abban Samha yace "David." Abba yace "Alryt Mr David, yar ka ta dawo gida koh" kallonsa kawai Mr David ke yi, can yace "I don't get the question" Abba yace "I want to know if ur daughter is back home" Mr David yace "Noo, amma ai xa ku fi mu sanin ko ta dawo ko bata dawo ba, ba d'an ka ne ya tafi da ita ba, kuma ya aureta" Muryar Mahaifiyar Samha suka ji a kansu tana ma kallon Col sama.da kasa tace "Ehen, Oga Soldier how may we help you kun dawo min da yarinya ta ne ko yaya?" Mikewa Col yyi yace "Ae yar taku bata gun d'a na kuma, shine na xo to find out ko ta dawo maku ne...." Daga haka ya mike yace "I leave you both in peace" da gudu tace "Ban gane basa tare ba malam..." Col ya juyo ya kalleta yace "Ba sai kin gane ba, but just know that my boy is back alone" daga nan bai kuma saurarenta ba ya fice, ta dinga juya maganan a kai wai his son is back, toh ita samanthan fah, kallon Mr David tayi kafin ta wuce ciki da sauri, shi kam komawa yyi ya xauna ya dau wayarsa ya shiga kiran layin Abuturrab, amma har ya katse ba a dauka ba, Rachael ta fito da dankwali daure kanta ba tare da tace ma mai gidan nata komai ba ta nufi gate, gidansu Abuturrab ta wuce, dai dai lkcn da Ummi da Hajiya Mariya suka iso gidan, kallon Ummi tayi tace "Kin ga mahaifiyar yarinyar can" Ummi dake ta kallon Rachael dake tsaye soldiers din bakin gate basu bar ta ta shiga ba, Hajiya Mariya ta fito sannan Ummi suka nufi gate din, Rachael na ganin Hajiya Mariya tace "Yauwa ji nayi wai tantirin d'an ku ya dawo ashe, to ina ya baro min 'ya ta?" Hajiya Mariya tace "Ehh toh, xa mu iya komawa asibiti ki tambayesa" Ta hade gira tace "In je asibiti in tambayesa kuma, asibiti ya koma rayuwa?" Hajiya Mariya tace "Kwarai" Ummi dai sai kallon Rachael take, Rachael tace "Toh ae sai mu je, don wnn karan idan na yrda shegiya nake, ba soldier ba, idan ma mala'ika ne ubansa ba yrda xan ba" Ummi tace "Subhanallah, Madam bai kai ga haka ba" A tsawa ce Rachael tace "To God who made me ya kai haka" Daga nan ta nufi mota fuu, Hajiya Mariya ta kalli Ummi tace "Hajiya mu je kawai" Daga haka suka bi ta, Tana biye da su a baya bayan sun isa asibitin fuskar nan nata a murtuke har suka iso ward din da Abuturrab yake, Shariff ne ke ta kwantar masa da hankali, shi kam ya jingina da bango idonsa lumshe har lkcn xuciyarsa bai bar xugin da yake ba, wani lkcn kuma yaji gabansa yyi mugun faduwa, Maganganun Ummi ne yyi tasiri kansa har ya d'an samu nutsuwa amma ya kasa cewa komai har sannan, Mami kuma na xaune kusa da shi tare da su Ramla dake kallonsa cike da tausayi, Rachael na fadowa ward din ta nufesa tana kare ma ruwan dake hannunsa kallo tace "Where is my daughter???" Bude ido yyi yana kallonta bai iya yace komai ba, ta iso gabansa sosai, a fusace tace "Nace ina 'ya ta" lkci daya idanuwansa suka kada a hankali ya dinga kai hannunsa kirjinsa, Dr Shariff ya mike yace "Madam don Allah ki bar nan, ba ki ganin condition dinsa ne....." Tsawa tayi masa tace "Bbu inda xanje ya fito min da Samantha, ya xa ayi ya dawo shi kadai batun ba shi kadai ya tafi ba, ina ya baro min 'ya ta kashe min ita yyi ko sayar da ita" tana kai wa nan ta fashe da kuka sosai tana tafa hannu tace "Ohh jesus what have i done to deserve this, gashi ya dawo bbu 'ya ta, kila ma ya kasheta ne, kila mutuwa tayi" tana kai wa nn Abuturrab ya tuge alluran hannunsa ya sakko daga kan gadon xai fita dakin, Shariff ya rikosa, wani kara da ya tsorata Rachael yyi ya tura Shariff xai fita da sauri Ummi ta rikosa tace "Are you on ur right senses Aliyu, baka da hankali ne, baka ga halin da kke ciki ba, ina xaka??" Tun jiya sai a lkcn hawaye ya shiga sakko masa ya rungumeta cikin raunin Murya yace "Mami ban san halin da take ciki ba, ban san inda ta tafi ba, you know her condition Mami, i can't take this any longer ji nake kamar xuciyata xata buga, it's hurting me" jansa tayi ta xaunar da shi kan kujera cike da tausayinsa take "Na fa ce xa a ganta boy, kai ba musulmi bane, me yasa baxa ka sa dangana a xuciyarka ba, in shaa Allah duk inda take tana lafiya kuma xata dawo gare mu" Rachael dai sai kallonsu take uwa idanuwan nn xa su yi magana, can dai ta fice bata xame ko ina ba sai gun Priest. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 86____87 Rachael na xaune parlon preist din har ya sallami b'akin dake tare da shi, ta mike ta dawo kujerar dake gefen tasa tace "Na gaishe ka father" Yace "You re blessed Rachael" tace "Amen father" ta d'an marairace tace "Akan maganar 'ya ta ne na taho gare ka, shi dan iskan da ya gudu da ita ya dawo jiya amma ban da ita, ban gane ma'anar hakan ba Father" Bai ce komai ba na kusan minti biyar, sai kuma ya mike ya shiga wani daki dake parlorn, Rachael ta gyara xama tana jiran fitowarsa, gaba daya hankalinta ya gama tashi, to ina Samantha tayi? Bayan kusan minti goma ya fito ya xauna yace "Rachael Addu'an da aka yi bai yi tasiri kan yaron ba gaskiya, wanda hakan na nufin shi ma iyayensa basu bar sa haka ba, sai dai kuma a kan ita 'yar taki addu'ar ya fada, she is the one making the man's life miserable, kuma a yanxu duk son nan da take masa bbu shi, wnn shine dalilin ma da ta bar sa tayi wucewarta" Rachael ta dafe kirji tace "Toh ina tayi father? Shi fa yanxu haka yana asibiti tare da iyayensa yana jinya, wai jinyar rashinta uwa shi ya haifa min ita, to amma ba wai damuna wnn yyi ba, babbar damuwata ina Samantha tayi?" Priest din yace "I can't say Madam Rachael, sai dai kuma ga wani labari mara dadin ji...." Bai kai aya ba ta sakko kan kujerar tace "Na me father?" Yace " 'yar ki ta bar Christianity, ta bar addinin gaskiya" Mikewa Rachael tayi, tayi wani uban k'ara tace "God forbid, it's not my daughter's portion, Samantha ta bar addininmu? Ta koma wani addinin? Nooo priest do something plss, da wnn abun kunyar gwara in yi sacrificing dinta, gwara a yanke min ita a gabana, tayi kadan wllh, sai na toxartata...." Sai kuma ta fashe da kuka sosai tace "Jesus Why me, what have i done to deserve this, priest da nasan haka Samantha xata xamar min da na kasheta tun tana ciki, yanxu bbu wani abinda xaka iya min?" Yace "Sai dai mu bar ma Jehovah komai....." Tace "Nooo, ban bar masa ba, priest for the sake of Mary ka kuntata min Rayuwar Samantha, ka mayar min da hankalinta gida kwanan nan in san abun yi da wuri" Yace "Xa ayi kokarin yin hakan" Mikewa tayi tana huci tace "Xan dawo very soon father, Jehovah ya kara girma" daga haka ta fice daga parlon tana tunanin irin yanda xata yi da Samantha idan ta shigo hannunta, tana sauka gida ta ci karo da Anty Maryam xaune da mijinta a parlor, Karasawa parlon tayi fuskar nan nata a murtuke tace "Makira annamimiya, munafuka.... uwar me ya kawo ki gidana, kinyi nasarar jefa 'ya ta cikin halaka kuma kema sai nayi ynda nayi na jefa ki cikin halaka, Allah ya isa tsakanina dake Maryam, ki cuceni kin ci amanata don da sa hannunki a duk abinda ya sami Samantha" Mr David da yake kallonta da mamaki yace "Haba Rachael, meye haka kike yi don Allah" a tsawace tace "Rufe min baki, wa ya sani ko kai ma har da hadin bakin ka tunda addinin naka ma ba wani damun ka yyi ba David, tun wuri Maryam ta bar min gida kada in mata abinda bata yi xato ba, ta fitaaa" Mr David yace "A'a ba gidan ki bane nn Rachael, kar kuma ki mance matsayin Maryam gu na...." Mikewa Anty Maryam tayi tace "Yaya bari in je, xa mu yi waya idan ban gane gun ba" Daga haka tayi ficewarta Rachael ta bi ta tana xaxxaga mata xagi har gate tana cewa sai ita ma ta bar addininta ta koma bautan Rana, ita dai Anty Maryam uffan bata ce ba har ta bar gidan, Rachael ta fashe da kuka tace "Jesus where have i gone wrong, why my daughter Rebecca??" Can ta share hawayenta tana murmushi tace "I will make dem regret everything, sai dai idan ba the God of Abraham nd Joseph nake bauta ma ba" Anty Maryam na isa titi ta kira Ummi, Ummi na daukan wayar suka gaisa tace "Hajiya dama na taho kano ne, kuma yayana yace min kuna asibiti, address din asibitin xa ki turo min" Ummi tace "Toh shknn Maryam, bari in turo" daga haka ta katse wayar, bayan kusan minti talatin Anty Maryam ta isa asibitin, Ramla ce ta fita shigo da ita, Anty Maryam na ganinta ta gane kanwar Aliyu ce ganin kamar da suka yi, Ramla ta gaisheta ta amsa snn suka shiga cikin asibitin, da sallama Anty Maryam ta shiga ward din, Ummi tace "Sannu Maryam" ta d'an kirkiri murmushi tana kallon Mami dake mata sannu da xuwa ita ma ganin kamanninsu da Abuturrab, gaishesu tayi gaba daya ta karasa bakin gadon tana kallon Abuturrab dake bacci, tausayinsa taji har ranta, cikin sanyin murya tace "Allah ya basa lafiya" Mami murmushi kawai tayi, Ummi tace "Ameen" Ilham ta kawo mata kujera ta xauna, Ummi tace "Saukar ki knn daga kaduna?" Ta girgixa kai tace "A'a naje gidan yayan nawa, shi ma ya fadi min kuna asibiti" Ummi tace "Ayya, sannu ya hanya?" Tace "Alhmdlh" daga nan Anty Maryam tayi shiru ta rasa abinda xata ce kuma, Ummi tace "Sai kika ji wannan lbrin mara dadi" a hankali tace "Wllh fa Hajiya, amma ina jin ba yin kanta bane, kila uwar ta ce tasa hannu, don nasan halin Samha" da mamaki Ummi tace "Allah?" Anty Maryam tace "Wllh kuwa yanxu ma sai kin ga rashin kirkin da ta min a gidan yayan nawa, har tana ikirarin nima xan gani" Ummi ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh Allah ya fi ta" Anty Maryam tace "Haka ne" Mami tace "Allah ya kyauta" Duk suka ce "Ameen" Shiru duk suka yi dakin. Sai kusan la'asar Mami da Ummi suka koma gida, bbu ynda basu yi da Anty Maryam su je can gidan tare ba tace A'a ita tana nan, dole suka tafi suka bar ta tare da Hajiya Mariya, khaleesat ta taho masu da abinci. Karfe biyar saura Abuturrab ya bude idonsa a hankali, rufewa yyi don ba kadan idanuwan nasa suka yi masa nauyi ba, tun da aka yi masa alluran bacci yake bacci sai lkcn ya tashi, mikewa xaune yyi a hankali ya kuma bude idon, Anty Maryam dake ta kallonsa tace "Sannu Aliyu" kallonta yake shi ma, cikin sanyin murya yace "Anty" tace "Na'am, how you feeling now" bai iya yace komai ba, ta dawo kusa da shi tace "Plss Aliyu ka kwantar da hankalinka ba yin kan Samha bane wnn, her mum is after you pple shi yasa da na xo kwanaki nace ka dage da azkar, duk inda Samha take i know she's fine kuma xata dawo gare mu soon, na Allah basa karewa a duniya in shaa Allah tana hannun na kwarai" tun da ta fara magana bai iya yace komai ba, Hajiya Mariya tace "Kuma ranan da abun xai faru sai da na kirasa nace masa i had a dream that's nt encouraging ya rike addu'a fah, sai ga wnn mummunan labari, ki gaya masa ko xai ji ta taki, mu har mun gaji da magana, da kuruciyarsa xai siyar ma kansa ciwon xuciya ba ma hawan jini ba" da mamaki tace "Ciwon xuciya kuma Hajiya" Hajiya Mariya tace "Wllh kuwa" rike kansa yyi da kyar yace "Mum condition dinta ne ke damuna, i..." Sai kuma yyi shiru, Anty Maryam tace "Don't worry about dat Aliyu, they re kindhearted people round the world, baxa su bar ta ta cutu ba, yanxu kawai addu'a xa mu dage yi har Allah ya karkato mana da hankalinta gida" cikin sanyin murya yace "Toh shknn Anty" sai kusan magrib Hajiya Mariya da Anty Maryam suka wuce can gidansu Abuturrab bayan Abbansa da abokinsa Col Ishak sun shigo ward din. Washegari misalin sha daya aka sallamosa a clinic ganin ya kwantar da hankalinsa sosai, aka daurasa kan drugs da injections, karfe sha biyu Ummi ta koma gombe da xumar xata dawo jibi dubasa, Dr Sharif dama tuni ya koma sbda clinic, gidan ya rage daga Anty Maryam sai Hajiya Mariya da wata frnd din Mami, Abuturrab na kwance bedroom dinsa idonsa lumshe kmr me bacci, he is just tryn his best ya yakice damuwar xuciyarsa, yana kuma assuring kansa Samha nd her babies are fine kmr ynda Anty Maryam ke yawan gaya masa, bude kofar bedroom din aka yi, ya bude ido a hankali, mikewa xaune yyi ganin Sadeeq tsaye bakin kofar, ya wara ido yace "Omg, you?" Tashi yyi daga kan gadon ya karasa ya rungumesa yace "Waow, am happy seeing you Sadeeq" Sadeeq yace "Batun ka mance ni guy" Abuturrab yace "Ni na isa, kana raina kullum son of a soldier" Dariya Sadeeq yyi suka karasa dakin, yace "Hope you re feeling much better yanxu" Abuturrab ya shafa kai yana murmushi karfin hali yace "Not without my wife Sadeeq" Sadeeq yace "Yea it's Sad frnd, but ka kwantar da hankalin ka, i knw she is fine, Allah xai dawo da ita hale nd hearty, we just have to pray hard" a hankali Abuturrab yace "Yea, sure" sosai Abuturrab yyi farin cikin xuwan Sadeeq ganin he is staying with him for sometimes, ji yake kmr an yaye masa damuwarsa ne xuwansa, bai san duk handwork din Abbansa ne don bai son ganin tilon d'an nasa a damuwa, ya so Mujaheed na kasar yasan shi ma baxai bar sa haka ba, washegari Anty Maryam ta wuce bayan yayanta ya xo har gidan sun yi sallama tunda gidansa yafi karfinta yanxu, har dakin Abuturrab ya shiga dubasa, daga haka ya fito suka yi sallama da Col ya fita da kanwar tasa, Anty Maryam bata tafi ba sai da ta tabbatar ta d'a d'a kwantar ma da Abuturrab hankali sosai. A can shagari qtrs kuwa Noor kmr yanda suke kiranta xaune take hankalinta kwance, bbu abinda aka raga ta da shi a gidan, yanda Umma ke ji da ita sai ka rantse jininta ce, haka ka yaranta da surkanta, shi kansa mai gidan tamkar yar cikinsa ya dauketa, halinta dai na rashin son magana na tare da ita har lkcn, hakan yasa Umma ke ganin taki sakin jiki har lkcn, Sumayya me koya mata addu'o'i da karatun qur'an har mamakin irin ynda take daukan karatu da sauri take, ranan dai ta kasa daurewa tace "Amma Anty Noor kina yawan karatun qur'an koh?" Murmushi Noor tayi tace "At times" Sumayya tace "Uhm no wonder, all the same, you've got a sharp brain, you very intelligent" nan ma Murmushi Noor tayi bata ce komai ba. Wasa wasa yau sati uku rabon Abuturrab da Samha ban da Sadeeq dake tare da shi, shi dai yasan da tuni ya xauce, har lkcn yaki kwantar da hankalinsa don ma yana kan medication, gani yake kmr abu ya same Samharsa ne, kowa a gidan yasan dauriya ce kawai yake don magana ma sai ya kwana ya wuni bai yi ba cin abinci kuwa ya xame masa tamkar babban aiki, duk ya rame sosai, kullum cikin kirga kwanakin haihuwar Samha yake, Duk weekend Ummi kan xo dubasa ta koma a ranan, sai ka rantse tare Mami ke jinyar da Abuturrab don ita ma ta rame, tausayin d'an nata duk ya hanata sukuni gani take kamar xata waye gari wataran ta rasa shi, tunanin hakan kan sa ta kuka kusan kullum, ko da yaushe addu'arta Allah ya dawo da Samha ko Aliyunta xai dawo yanda yake da, Sau da yawa Abba kan kirasa bedroom dinsa ya xaunar da shi duk da ba magana xa su yi ba, kwanciyar hankalin Abba daya har lkcn Yakumbo bata san Aliyu ya dawo ba tana can Adamawa, ba ita kadai ba har yan uwansa gaba daya bbu wanda ya fadi ma ko da wasa, kullum kuma addu'a yake kada Allah ya jefota gidan bbu notice. Ranan wata Asabar Abuturrab na kwance kmr mai bacci sai dai ba baccin yake ba, Sadeeq kuma na xaune yana operating laptop Ummi ta shigo dakin da sallama, Sadeeq yace "Sannu da xuwa Ummi" tace "Yauwa Sadeeq bacci yake?" Sadeeq ya kallesa yace "Ba wani bacci idonsa biyu tun safe yake a haka, always pretending" Ummi ta karasa ta xauna gefen gadon tana kallonsa, Sadeeq kam sai kallon warce suka shigo dakin tare da Ummi yake, can dai tace "Ina kwana" ba tare da ya kuma kallonta ba yace "lfya lau" Ummi tace "Boy" a hankali ya bude ido, ya kirkiri murmushi yace "Welcm Mami" tace "Baka cin abinci boy koh?" Mikewa xaune yyi yace "Mami tambaye sadeeq na karya daxu" Sadeeq yace "Noo plss ba wani Sadeeq, you think am daft ko, toilet fa ya xubar da shayin Ummi, potatoes da egg din ma da xaki daga gado xaki gansu, sai dare yyi ya faki ido ya kwashe ya xubar, which is very bad of him" Xaro ido Abuturrab yayi yana kallonsa can yayi dariya yace "Sa ido sana'a mara amfani" Sadeeq ya bude hannu yace "Noo ba wani sa ido, da ina sa maka ido da ai baxan bari kke xubar da abinci ba, yanxun ma naji xaka yi karya da sunana ne shi yasa na tona" Ummi ta kalli Sadeeq tace "But you re nt doing him good kana barinsa baya cin abinci Sadeeq" Sadeeq yayi dariya yace "Ummi it's a deal muka yi da shi ae" Hararansa Abuturrab yyi yace "Wani deal bayan gashi kana sa idon har ynxu" mikewa sadeeq yyi yace "Nan gaba abba xan dinga shigowa da ina daga masa karkashin gadon yaga almunbazzarancin da kke masa da abinci" daga haka ya fice daga dakin yana wani irin murmushi, Ummi tace "Alryt, pls pls Boy ka dinga cin abinci kaga yanda ka rame kuwa am not happy gaskiya, to ko Samhan ta dawo ynxu ai ba gane ka xata yi ba wllh, u have changed totally, haba Aliyu" Murmushi yyi bai ce komai ba, sai a snn suka hada ido da fatima dake ta kallonsa, ta sunkuyar da kanta tace "Ina Kwana?" Ya kirkiri murmushi yace "Lafiya lau, ya hanya" kanta a kasa tace "Lafiya, ya jiki?" Yace "Alhmdllh" Mikewa Ummi tace "she said tana son xuwa ta dubaka shine muka taho tare sun yi hutu ne" yace "Alryt am grateful" fita Ummi tayi daga dakin, Fatima ta dago tana kallonsa a hankali tace "Am sorry Aliyu, it seems i caused everything, Allah ya bayyanar da ita lafiya" Bai iya ya kalleta ba yace "No you caused nothing, haka Allah ya tsara, after all, there is always a reason for everything, God plans best you knw" gyada kai tayi tana kkrin mayar da hawayen idonta, yace "Ya su Khadijah da Rabi'ah?" Kanta a kasa tace "They are fine" Daga haka ta mike ta kwashe kwanukan dake dakin ta nufi kofa ya bi ta da ido har ta fita, karfe uku Ummi ta fara shirin komawa gombe, Mami tace "Hajiya baxa ki bar fatima ba tunda kince sun yi hutu" Ummi ta kalli fatima dake tsaye sakale da handbang dinta har ta shirya tace "Bata taho da kaya ba ai Hajiya" Mami tace "Ba ga kayansu Ramla ba, ki bar ta tayi mana kwana biyu mana" Ummi tayi murmushi tace "Toh shknn." Yau ma kamar kwanaki biyun da suka wuce haka Noor ta tashi da ciwon baya, a kwanaki biyun bata bari kowa ya gane halin da take ciki ba, iyakar dauriya ta iya sa ba kadan ba, duk da Umma na yawan ce mata in dai taji ciwo a ko ina tayi magana sai dai tayi murmushi kawai, jin ta kasa kwanciyar kuma ta mike xaune da kyar, shima taji xaman na neman gagararta, tashi tsaye tayi ta durkusa don axaban ya mata yawa, bude kofar dakin aka yi Sadiya ta shigo rike da tray din breakfast don Umma bata bari ta sauka kasa, komai daki ake kai mata, Sadiya ta ajiye trayn da sauri tace "ya aka yi Noor?" Ta d'an kirkiro murmushi tace "Kai na ke d'an min ciwo" Sadiya tace "Toh bari a kira Umma" da sauri tace "A'a ai ba sosai bane, idan na sha tea sai in dau paracetamol" Sadiya ta durkusa ta shiga hada mata tea'an, duk da irin axabar da Noor ke ji bata bari ya nuna a fuskarta ba, ganinta a durkushe Sadiya tace "Toh ki xauna ki karya" gyada mata kai tayi tace "Toh" cike da karfin hali ta xauna taji kmr ana kara mata ciwon amma ko da wasa bata nuna ba, ta jawo cup din tea ta kai baki, ji tayi waist dinta ma ya dauka, ganin ta kasa shan shayin Sadiya tace "Are you okay noor" murmushin karfin hali ta kuma yi tace "Am ohk" Ae bata rufe baki ba taji wani mugun axaban da ya linke na wanda take ji, bata san lkcn da ta ajiye cup din ba ta runtse ido, mikewa sadiya tayi tace "Subhanallah" da sauri ta fice daga dakin, sai ga ta da Umma sun shigo, Umma ta dagota tace "Noor ba nace in kin ji ciwo ki min magana ba, ina ke maki ciwo" kasa cewa komai tayi don ciwon ya fara fin karfinta, can ta fara yarfe hannu hawaye na sakko mata, Umma tace "Sadiya maxa kira min yayanku mu tafi asibiti" da sauri Sadiya ta fita daga dakin don xuwa part din yayan nasu, Umma ta dauko hijab dinta ta sa mata, ixuwa yanxu sunan Umma kawai Noor ke kira don ita kadai tasan abinda take ji, Umma na rike da ita suka sakko parlor, tafiyar ma dauriya kawai take, Sadiya ta dawo tare da Maryam, haka suka fita waje, Maryam ta taimaka mata ta shiga mota Umma da sadiya ma suka shiga motar, Maryam ta shiga gaba, Mijinta dake ta yi ma Noor sannu ya tada motar suka yi asibiti. Kafin su isa asibitin har ta fita hayyacinta, tafiyar ma kasawa tayi bayan sun fito daga cikin motar ta kalli Umma cikin kuka tace "Wayyo Umma Aliyu, kuce ya xo" Umma ta kalli Maryam, Maryam dai ta kasa cewa komai sai kallon Noor take, da taimakon nurses din da Mijin Maryam ya kira suka shiga da ita asibitin sai labour room. Meanwhile Abuturrab kam tunda ya tafi masallaci sllhn Asuba har gari ya waye bai dawo ba, dole Abba ya koma masallacin ya taso sa a gaba suka dawo gida, Mami ta shiga bedroom dinsa tana kallonsa ganin damuwar dake fuskarsa ta xauna kusa da shi cikin raunin murya tace "Don't start that again Son, wai ya kake son inyi da raina ne, baka tausayina Aliyu, tun da Sadeeq ya tafi abun ka ya kara jagulewa kuma, haba son, ya kake son inyi da raina?" hawaye ne ya cika idonsa ya daura kansa a shoulder dinta cikin rawar murya yace "Mami Samha...." Rungumesa tayi ita ma hawayen ya cika idonta tace "I know son, musulmin kwarai fa an san sa ne da tawakali, sau nawa kuma xa ace maka tana hannun mutanen kwarai idan Allah ya yrda....." Da kyar yace "Mami her delivery may be today or tomorrow..." jikin Mami yayi sanyi, ta shafa kansa a hankali cikin sanyin murya tace "In sha Allah xata sauka lafiya albarkacin wannan rana ta juma'ah, kayi ta mata addu'a kaji son" kai ya gyada mata bai iya yace komai ba. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 88.....89 Har kusan sha biyun rana Noor ban da wahalan labour bbu abinda take, bbu abinda ke kara daga ma Umma hankali irin ynda take kiran Aliyu gashi ta tambayeta ko tana da number sa taki cewa komai, in ta gaji da kiran Aliyu sai ta koma Mumynta da Abbanta, suna nan asibiti har kusan karfe biyar amma shiru, nan likitan ya kira Abbansu Sumayya don yana asibitin shi ma a lkcn yake gaya masa in har wasu awanni biyun suka wuce bata haihu ba to xa ayi mata Cs kar babies su samu matsala, shi dai rasa abun cewa yayi, can dai ya amsa ma likitan ya fita, Umma ya kira ya sanar mata yanda suka yi da likitan, ita ma tayi shiru duk jikinta yyi sanyi, girgixa kai yayi yace "Ina jin Hajiya gwara ki lallabeta ta bada number mijin nata a kirasa ko ya kika ga" tace "Haka ne" daga haka ta koma ciki, ta xauna kusa da ita ta kamo hannunta ta dago kanta, ji tayi kamar ta xubar mata da hawaye ganin yanda ta jigata, ta daure tace "Look at me Noor, ki gaya min gaskiya, kina da number Aliyun?" Noor ta daura kanta jikinta tana girgixa kai ta fashe da kuka sosai tace "Bani da shi Umma, don Allah ku kira min shi mutuwa xan yi wllh" Jikin Umma yayi sanyi ba kadan ba, to ita yanxu ina xa su fara nemo Aliyu? Usman d'an Umma na uku ne yasa aka debo masa ruwa a cup ya yi addu'a ciki ya ba Maryam ta bata, Umma na rike da ita ta kai mata ruwan baki ta kauda kai da sauri tace "Bana jin kishi Umma" Umma tace "Addu'a ne Noor, ki daure ki sha" da kyar ta bude baki ta sha ruwan, bayan kusan minti biyar ta d'an nutsu har ta samu bacci, ashe duk axaban da take ji na wasa ne don cikin baccin taji ciwon da ya linke wanda take yi tun safe, duk ta haukace masu, nurses suka dawo gunta da likita daya, hankalin Umma yyi mugun tashi haka Maryam da tausayinta yasa ta fita kawai, Umma ma dai ta kasa daurewa ta fita, ko minti biyar bata kara ba ta haifo yaranta maza biyu, kukansu ya cika dakin, Hawaye ne ya sakko idon Umma ta shiga gode Allah a xuciyarta, yaran ma basu wani jigata kmr yanda likitocin ke tunani ba. Bayan minti goma aka fito ma da su, Umma ta karbi daya, Maryam dake ta murmushi ta karbe dayan dake ta ihu, Kallon yaran Umma ke tayi ganin girmansu, ita kuwa Maryam tana ganin yaran tasan lallai mahaifinsu ma ba baya ba wajen kyau, tun da aka fito da Noor take baccin wahala, Su Abba da yaransa maza dama tuni suka koma gida ganin ta sauka lafiya har sun ga yaran, Sumayya da Sadiya suka taho asibitin da kayan shayi sai kallon fararen yaran Sumayya take, ta kalli Sadiya tace "They r so cute kamar larabawa sis" Sadiya tayi murmushi tace "Wllh kuwa" sai bayan isha Noor ta farka nan da nan Umma ta hada mata shayi ta bata, da kyar ta dinga shan shayin har ta shanye, Umma tace "Sannu Noor, baki tambayi yaran ki" sunkuyar da kai tayi bata ce komai ba, Anty Maryam tayi murmushi ta dauki yaron dake kwance a gadon yara, farida ma ta dauko dayan suka nufota, gaba daya yaran suka ajiye mata a jiki, kallonsu kawai Noor take ganin su wasu kanana don bata saba ganin jarirai ba, banda dogon hancinta da ya fi na babansu bbu abinda suka dauko nata, sak Aliyu kamanninsu har hasken, irinsu kuma ake kira da identical Twins tsabar basu da bambanci, Farida ta nuna mata dayan da aka sa ma xare a hannu tace "Kinga Hassan ga Hussaini" bata san lkcn da murmushi yyi escaping lips dinta ba sae dai kuma ta kasa daukan yaran sbda kunyar Umma duk da ba ma iya daukansu xata yi ba, Umma tayi dariya tace "Amma gaskiya basu yi kama da ke ba sai dai Aliyu" rufe fuskarta tayi, Maryam tayi dariya haka ma farida, Sadiya tace "Xan so in ga Aliyun nn ni kam" Noor bata iya ta bude fuskarta ba sbda kunya, Umma tace "Toh kin dai san gidansu Aliyu a nan kanon koh?" Shiru Noor tayi bata ce komai ba, Umma tayi murmushi tace "Kya ma bude baki yarinya" A nan asibitin Umma tayi ma yaran wanka tunda kwana xa su yi, da kanta ta kai Noor bayi ta taimaka mata ta dauraye jikinta da ruwan xafi kafin su je gida. Washegari misalin tara aka sallamesu, suna isa gida wanka mai lafiya tayi ma Noor snn tayi ma jariran da suka cika gidan da ihu don tun jiya bbu abinda aka bari aka basu a asibitin sai ynxu da suka dawo gida, Noor na xaune tana kallon ynda Umma ke shiryasu, gani take kmr da an taba su xa su iya karyewa, nan ko su Umma ganin girman yaran suke sosai, da yake ita bata saba ganin jarirai ba bata san girmansu da rashinsa ba. Umma na gama shiryasu sai ga Abba ya shigo nan ya kuma yi ma Noor da ta kasa dago kanta barka, ya dau yaran gaba daya yayi masu addu'a snn ya fita, Ahmad da su Usman ma suka shigo suka mata barka suka ma yaran addu'a su ma suka fita, Anty Maryam ce ta shigo da warmer din pepper soup na kayan ciki ta ajiye dakin tana cewa "Sannu mai jego" murmushi kawai Noor tayi, Umma ta dau hassan ta daura ma Noor a kan kafa ganin da gaske bata iya daukan jariri ba dan tun a asibiti bbu wanda ta dauka sai dai tayi ta kallonsu, Umma tace "Toh fito da maman in ga ko xai karba" Noor ta kasa yin abinda Umma tace sbda kunya, Maryam ta bude mata zip din rigar jikinta, da kyar ta yrda tayi hakan don kunya take ji, ita tunda take ko Mumynta bata yrda ta ga tsaraicinta da girmanta ba banda Abban twins dinta sai Umma ynxu, Umma na xaune kusa da ita har ta ga babyn ya fara shan abincin snn tayi murmushi tace "You now feel the joy of Motherhood dear, Allah ya raya maki su a bisa tafarkin Islam" Noor bata iya ta dago kanta ba, bayan minti uku Umma tasa ta mayar da shi daya side din, sai da ta tabbatar abincin ya isa babyn snn ta dau d'an uwansa shi ma tasa ta bashi, bayan ta gama da babies din ta kwantar da su gefe, da kanta ta xuba mata naman kayan ciki da Maryam ta kawo mata ta dauka ta bata, tana gama ci ta sha magungunanta da aka bata a asibiti snn ta kwanta. Da yamma misalin biyar Ahmad ya shigo dakin tare da Maryam, bayan sun gaisa ya dau Hassan yana kallon Hussain yace "They re really identical, in ji an banbance maku su a asibiti" Umma tace "Hassan din ne a hannunka" yace "Maa sha Allah" kallon Noor yyi yace "Maman biyu bani number mai gidan ki" shiru tayi tana kallonsa, can a hankali tace "Bani da Number sa" Umma tace "Baki da numbersa kuma Noor, you've punished him a lot dear nasan duk inda yake yanxu baya da kwanciyar hankali" kamar xata yi kuka tace "Umma wllh bani da numbersa da gaske" Ahmad yace "Toh kin san gidansu ai koh?" A hankali ta gyada kai, yace "Toh bani address" bata ce komai ba har sae da Maryam tace "Ki bada Noor" kallon Umma tayi tace "Xan rubuta a takarda" aka dauko mata takarda da pen ta rubuta ta mika ma Maryam ta karba ta ba mai gidanta, babyn hannunsa ya kwantar yace "Ya sunan mai gidan naki?" Noor ta sunkuyar da kai tace "Doctor Aliyu" Umma tace "Oh likita ne" Noor tace "Uhm" Ahmad yace "Alryt to, bari in je" sallama yyi masu ya fita. Karfe biyar da yan mintuna Ahmad ya isa dai dai gate din su Abuturrab, ya juya ya kalli Usman yace "I think it's here" bude motar suka yi a tare suka fito suka nufi gate din gidan, Usman ya d'an tura gate din yaji a rufe, bude gate din aka yi, suka ga wani da khakin soldier tsaye, Ahmad yace "Barka da Yamma" Sojan ya amsa masa, Ahmad yace "Tambaya muke don Allah, sorry for the inconvenient, pls akwai Dr Aliyu a gidan nan?" Sojan yace "Eh, yaron mai gidan kenan" Ahmad ya shafa kai yace "Toh madallah ko xa a yi mana sallama da shi pls" Sojan yace "Daga ina ku ke?" Yace "Shagari qtrs" Rufe gate din sojan yyi, Usman ya kalli Ahmad yace "Lallai!! ko waye mai gidan" Usman ya koma gun motarsu yace "Babba ne tun da kaga haka" bin bayansa Ahmad yyi suka tsaya jikin motar, tsayuwar kusan minti goma sha biyar suka yi basu ga an bude gate ba, Usman yace "Anya nn ne gidan kuwa bro, dubi fa ynda aka shanya mu nan" Ahmad yace "Cool down, let wait a little more" bude gate din aka yi sojan ya fito yace "Xa ku iya shigowa" Ahmad yace "Toh godiya muke" daga haka suka bi bayansa suka shiga compound din, sae a snn suka ga sojoji hudu a compound din, gaishe su suka yi, Sojan ya nuna masu karkashin wani Artificial tree mai dauke da kujeru uku yace "Ku jira sa a can" godiya Ahmad ya kuma yi masa snn suka karasa suka xauna suna kare ma makeken compound din kallo, kamar bai son taka kasa haka ya dinga tahowa har ya iso inda suke xaune, gaba dayansu biyun kallonsa suke, ya d'an yi murmushi yyi masu sallama ya ja kujera ya xauna, suka amsa sallamarsa snn aka gaisa, Ahmad ya kalli hannunsa dake dauke da alluran drip yace "Baka da lfya?" Abuturrab yace "Yea, amma naji sauki Alhmdllh" gaba dayansu suka yi masa Allah ya sauwake, Ahmad ya d'an sauke ajiyar xuciya don ba ma sai ya tsaya dogon tambaya ba ya ga kamannin twins din Noor sak tare da Abuturrab, Shi kansa Usman kallonsa kawai yake, nan da nan kuma yaji tausayinsa don kana ganinsa kasan bai da isasshen lfya, Ahmad yyi breaking silent din yace "Dr Aliyu right?" Abuturrab ya kallesa yace "Yea, sai dai bn gane ku ba" Ahmad ya d'an yi murmushi yace "Ehh baka san mu ba dama Dr, mu ma kuma bamu sanka ba, sai dai mun gane ka ta dalilin carbon copies dinka" kallonsu kawai Abuturrab ke yi don bai gane inda suka dosa ba, Ahmad da ya kula da haka yyi murmushi yace "Alryt Dr, mun jima muna jin lbrin ka, mun kuma xo neman taimako ne a gun ka sbda Allah" Abuturrab ya jinginar da kansa da kujera yace "Na me fa?" Usman dai sai kallon yayansa yake don bai gane what he is up to ba, Ahmad yace "Mara lafiya xaka duba mana mu biya ka ko nawa ka bukata doctor" Hade rai Usman yyi yana kallon Ahmad, to what's d meaning of this kuma, Abuturrab yace "Ayya Allah ya bada lfya, sai dai nima bani da lafiyan, am under medication ma na fito yanxu" Ahmad yace "It won't take long Dr, na ga alamar baka da lfya, but ka taimaka sai ka ga kai ma ka samu waraka gun Allah, mun baro asibiti da dama mun baro likitoci da dama muka taso takanas gun ka..." Mikewa Usman yyi don ransa ya gama bacewa yana kallon yayansa yace "Excuse me" daga haka ya bar gun don bai ga amfanin hakan ba, shi dai Abuturrab bai ce komai ba, har ya mance rabon ya duba patient, can ya kalli Ahmad yace "What's wrong with the patient?" Ahmad yace "Ka taba dubata da dadewa kuma an samu waraka a lkcn, i cnt say what's wrong with her" Abuturrab yace "Alryt, a ina ku ke?" Ahmad yace "Shagari qtrs" Abuturrab yyi shiru, can yace "It's kinda far, anyway bari in shiga in fito" Ahmad yace "Toh mun gode Dr, Allah ya yaye maka damuwarka soon" kallonsa Abuturrab yyi kafin yace "Amin" ya shiga ciki, murmushi Ahmad yyi a xuciyarsa yace "Buh he is kind of nyc, he have got a free heart, bai ji tsoron ko cutarsa xa mu yi ba ya yrda xai bi mu duba mara lfya" text ne ya shigo wayar Ahmad ya duba yaga Usman ne, bude content din yyi yaga text din kmr haka, "Haba bro, hakan bai da amfani just tell him what we re here for mu bar nan, stop playing with his sense ko kai ake ma haka baxa ka ji ddi ba" Ahmad bai tanka text din ba sai ma murmushi da yyi, Abuturrab na shiga ya sanar da mami xai je duba patient a shagari qtrs an kira sa, taji ddin jin hakan sai dai kuma yanda taga yanayin jikinsa tace "Buh you re weak son, haka xaka fita gashi ko karewa ruwan bai yi ba" Yace "Worry not Mami, xan iya da baxan iya ba baxan je ba ai" tace "Toh shknn Allah ya tsare" yace "Ameen" drip din hannunsa ya cire, ya sauya jallabiyar jikinsa xuwa kananun kaya snn ya fita, har lkcn Ahmad na nan yanda ya bar sa, ya karasa yace "Am ready" mikewa Ahmad yyi yace "Alryt Dr" daga haka suka fita gun mota, Ahmad ya xauna maxaunin driver, Usman dama na xaune gaban motar, Abuturrab ya bude baya ya shiga. Har suka isa Shagari qtrs bbu wanda yace komai cikinsu, Ahmad yyi parking a compound din snn ya fito yana kallon Abuturrab da ya fito daga motar yaji gabansa na faduwa haka kawai, Ahmad yace "Mu shiga Dr" bin bayansa yyi, Usman ma na biye da su a baya har xuciyarsa ya dinga jin tausayin Abuturrab ganin bai ma yi tunanin ko cutarsa suka kawo sa nn su yi ba ya biyo su da xuciya daya, Xama Abuturrab yyi a babban parlon gidan, Ahmad na murmushi yace "Welcm to our home Dr" Abuturrab ya mayar masa da murmushin, Usman ya wuce ciki sai ga sa sun fito da Umma, tun da ta shigo parlon take kallon Abuturrab, a xuciyarta tace Eh lallai twins sun yi ma Noor wayo, Abuturrab ya kalleta yyi kasa da kai yace "Ina yini mama" xaunawa tayi tace "lafiya lau" mamaki take a xuciyarta anya me innocent face din gabanta xae iya aikata abinda Noor tace, ta kawar da tunanin da wuri tunawa da tayi abun ba a fuska take ba, Umma tace "Sannu da xuwa Aliyu" ya kalleta da mamaki jin ta kira sunansa, can ya sunkuyar da kai yace "Nagode mama" Mikewa tayi ta wuce ciki, ba a dau lkci ba sai ga Maryam ta fito rike da Hassan, Ahmad ya mike ya karbi yaron ya isa kusa da Abuturrab ya mika masa yana kallonsa, kallon jaririn Abuturrab yake kafin ya karba yace "Oh dama baby xa a duba, buh am nt an expert a wnn bangaren, they shud have take....." Shiru yyi yana kallon jaririn lkci daya gabansa ya tsananta faduwa, Usman ya karbi hussain da Sadiya ta fito da ya nufi gun Abuturrab shi ma ya mika masa a hannunsa, Abuturrab ya kallesa shi ma, can ya dago a hankali yana kallon occupant din parlorn, ganin irin kallon da suke masa gaba daya yace "Noo" lkci daya ya mike ya ajiye yaran gaba daya kan kujera ya nufi Ahmad ya rikosa cikin rudewa yace "Noo plss, I want to see their mother, where is...." Makalewa sauran maganan yayi ganin Samharsa da yyi tsaye bakin stairs ta ki karasowa parlon tana wasa da fingers dinta kanta a kasa, wani mugun bugu xuciyarsa yyi, ya dafe kirjinsa da sauri, lkci daya ya fara ganin jiri, idonsa ya fara juya masa, Ahmad ya nufo sa da sauri ganin yanayinsa, kafin ya iso tuni yyi kasa har lkcin yana rike da kirjinsa da duk hannunsa biyu, Ahmad ya rikesa yana salati, Rudewa Umma tayi haka su Maryam, bbu abinda ya kuma rikitasu sai irin karan da Noor ta saki, ta taho parlon da gudu ta durkushe kusa da shi ta rikesa cikin tashin hankali tace "Doctor....." Haka ta dinga kiransa tana jijjigasa, Umma ta janye ta su Ahmad kuma suka fitar da shi daga parlon sai asibiti. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 90..... Har aka yi magrib Abuturrab bai bude ido ba duk da alluran da aka yi masa, Ahmad na tsaye cikin ward din da Usman Abbansu kuma na gun likita, sai a snn ya fara daya sanin k'in gaya masa da yayi tun a gida, kilan da duk hakan bai faru ba, Noor dai na xaune kusa da gadon da Abuturrab yake ta hade kanta da gadon, a hankali take kuka wanda su da suke tsaye dakin ma basu san abinda take ba, Abbansu ne ya shiga da sallama yana kallon Ahmad yace "Bbu waya tare da shi ne?" Usman ya mika masa wayar Abuturrab dake hannunsa, Abban yace "Ka ba Ahmad, ya kamata a kira can gidan nasu" Ahmad ya karbi wayar ya shiga contacts yana duba number da ya kamata ya kira, bbu wasu contacts a ciki da yake ba main sim dinsa bane, ganin wani number da aka yi saving da Mum kawai yyi dailing, yana fara ringing Hajiya Mariya ta daga tace "How you my son..." Ahmad yace "Ina yini mama" Hajiya Mariya ta d'an yi jim, can tace "lafiya lau" yace "Dama Aliyu ne ke asibiti...." A rude tace "Asibiti? kai waye?" Bai amsa tambayar ba, ya dai fada mata sunan asibitin, bata kuma cewa komai ba ta katse wayar ta shiga kiran Mami da sauri, Mami na dagawa tace "Yaya wai kin ji ynxu aka kira ni Aliyu na asibiti, ya fita gida ne?" Kasa cewa komai Mami tayi, Hajiya Mariya ta dafa kanta tace "Pls ki kwantar da hankalin ki yaya, ki gaya ma Col sai ku taho asibitin tare nima gani nn xan fitowa ynxu" har ta katse wayar sai ta tuna bata fadi asibitin ba ta kuma kiranta ta gaya mata snn ta dau makullin mota ta fita da sauri. Ana kiran Isha suka iso asibitin kusan a tare har da Col da yyi driving din da kansa, kallo daya xaka yi ma Mami ka tausaya mata, Hajiya Mariya ta fito daga motarta ta nufi tasu motar ta bude ma yayarta kofa, Mami ta fito, Hajiya Mariya tace "Don Allah ki kwantar da hankalin ki yaya, everything will be alright" ko kallonsu Abban Abuturrab bai yi ba ya nufi entrance din asibitin, Hajiya Mariya ta kama hannun Mami suka bi bayansa tana kkrin kiran layin Abuturrab yana ringing Ahmad dake tsaye har lkcn a ward din ya daga, nn ya gaya ma Hajiya Mariya ward din da suke, ganin Col ya nufi gun nurse dake reception Hajiya Mariya tace "Na kira fa su sun fadi dakin da suke" tsaye yyi har suka shiga gaba snn ya bi bayansu, suna isa dakin Shi ya murda kofar ya shiga sannan suka shiga su ma, bai ko kalli mutanen dake tsaye dakin ba ya isa gadon da Abuturrab yake ya rungume hannayensa yana kallonsa, Mami kam kasa karasawa tayi lkci daya hawaye ya shiga sakko mata, Hajiya Mariya tayi karfin halin gaida su Ahmad da dad dinsa dake tsaye ita ma ta karasa gadon tana kallonsa, har lkcn Noor na xaune kusa da gadon kanta kife kan gadon, duk da muryar Hajiya Mariya da taji ta kasa dagowa sai hawaye take, Girgixa kai Col yyi ya kalli Hajiya Mariya yace "We are leaving for india tomorrow in sha Allah" daga haka ya juya zai fita ta sha gabansa murya can kasa tace "Col ga bayin Allahn da suka kawo sa asibiti baka ko gaisa da su ba kuma xaka fita" sai a snn ya daga kai yaga su Ahmad dake kallonsa, karasawa yyi gaban dad dinsu ya mika masa hannu suka gaisa ya ba Ahmad da Usman hannu su ma, snn ya kalli dad dinsu yana kirkiran murmushi yace "Mun gode kwarai da kulawar ku Alhaji, Allah ya saka da alkhairi, though bn ma san ya fito gida coz he is under medication since yesterday," Ita kam Hajiya Mariya idonta na kan Noor tana mamakin wacece ita ganinta kusa da Abuturrab gashi tun da suka shigo bata dago ba, bude kofar ward din da aka yi yasa ta dauke idonta kanta tana kallon kofar, Umma ta shigo hannunta rike da Hussain, Maryam ma ta shigo rike da Hassan, Umma na hada ido da Mami jikinta yyi sanyi ganin ynda take kuka kuma ko ba a gaya mata ba ta gano ita ce Mahaifiyar Aliyu, ta karbi Hussain gun Maryam ta karasa kusa da ita ta mika mata yaran biyu, kallonta Mami take kafin ta kalli jariran sai kuma dai ta share hawayen idonta duk ta karbesu, Umma na murmushi a hankali tace "Ur grandchildren...." Mami ta dinga kallonta ko kiftawa bbu don bata gane inda ta dosa ba, can ta kuma kallon yaran gabanta na faduwa, Umma ta kalli Noor da taki dagowa har lkcn tunani ta fara yi to ko dama basu santa bane, ita ma bata san su ba, ganin confusion tattare da Mami, Umma tace "Yaran Aliyu kenan, ga kuma matarsa can...." Mami ta juya da sauri tana kallon wacce Umma ke nuna mata, Hajiya Mariya ta dago kan Noor da mugun mamaki, ae ko ta ga Samha ce, a hankali tace "Samha???" Noor da ta kasa dago kanta ta mike ta shige jikinta ta rungumeta tana shesshekar kuka, Hajiya Mariya da hawayen farin ciki ya cika idonta ta rungumeta ita ma tace "Meyasa kika mana haka Samha, ina kika tafi all this while," cikin kuka tace "Mumy nima bn sani ba" Col dake kallonsu gaba daya cike da mamaki ya kalli yaran hannun Mami, ya kuma kallon Abuturrab, kofa ya nufa dad din Ahmad ya bi bayansa, Ahmad yyi murmushi ya bi su shi ma da Usman, Hajiya Mariya ta janye Noor jikinta tana goge hawayen idonta tana murmushin farin ciki ta ja Noor gun yayarta tace "Mami kin ga Samhar Aliyu, Allah ya amsa addu'ar mu ya dawo mana da ita lafiya" Mami da ta kasa cewa komai hawayen farin ciki na sauka idonta ita ma ta dinga gyada ma kanwartata kai kawai, Hajiya Mariya ta karbi yaran gaba daya hannunta ita ma hawayen ya ki tsaya mata, a hankali Noor ta taka ta isa gun Mami har lkcn kanta na kasa ta shige jikinta, rungumeta Mami tayi wasu sabbin hawayen na xuba idonta ta rasa wani irin farin ciki xata yi, Su Umma da Maryam dai sai kallonsu suke cike da tausayi, Hajiya Mariya ta karasa gun Abuturrab ta kwantar masa da twins din kusa da shi, tana murmushi ta ja dogon hancinsa idonta cike da hawaye tace "C'mon wake up now Atturab, duk ka daga mana hankali ka mayar da mu hypertensive patients, ka tashi ga Samha ga babies dinka" tana magana ne hawaye na sakkowa idonta, hancinsa ta kuma ja tana girgixa kai tace "Atturab...." Ya bude ido a hankali yana kallonta, ta bude ido tayi wani murmushin farin ciki tace "You are back my only son" A hankali yace "Mum, mum Samha... I saw...." Runtse ido yyi jin kansa da ya wani sara masa, ya shiga kkrin mikewa xaune ta rikosa xata taimaka masa, Hussain ya tsala ihu ta dalilin dannesa da yyi da hannu, Ae noor bata san lkcn da ta janye jikinta a na Mami ba ta nufo gadon da sauri jin ihun yaron, suka hada ido da Abuturrab, a hankali ya sauke idonsa ya dauke hannunsa gun yana kallon yaran gefensa ya mike xaune, Maryam ta juya tana 'yar dariya can ciki, kunya ya ishe Noor ganin kallon da Hajiya Mariya ke mata, sunkuyar da kai tayi tana jan fingers dinta ta juya, Hajiya Mariya ta d'an yi jim ganin reaction din Abuturrab da ya ga Noor, to ko ya riga ya ganta ne, ta dai dau Hussain da ya ki yin shiru ta mika masa, a hankali ya sa hannu ya karbesa, nan da nan yaron yyi shiru, tayi murmushi tana kallonsa Murmushin gefen baki yayi shi ma, ya kai bakinsa kunnen yaron, bayan kusan minti uku ya ajiye sa ya dau dayan shi ma yayi masa haka, a hankali ya kwantar da shi kusa da d'an uwansa, ya sakko da kafafuwansa daga kan gado ya rike kai yace "I need rest mum" Umma ta karaso gun gado tace "A'a da ka jira sai an sallameka...." Ya kalleta ya d'an yi murmushi yace "Naji sauki Mama, nagode" ta kalli Maryam tace "Ki kira su Abba a waje" kofa ta nufa, Abuturrab ya d'aga kai yana kallon Mami dake tsaye inda take duk jikinta a sanyaye, murmushi ya sakar mata, murya can kasa yace "Mami" tayi karfin halin mayar masa da murmushin, sauka yyi daga kan gadon ya nufeta ya shige jikinta, cikin sanyin murya yace "Am... am sorry for all the troubles i cause you mother...." Shafa kansa tayi ta kasa cewa komai, Abbansa ne ya shigo dakin tare da Abban su Ahmad da su Ahmad din, suna hada ido da shi ya sunkuyar da kai, can kuma ya nufesa duk jikinsa a sanyaye, barin wajen col yyi ya nufi gun Umma yace "Amm... Mun gode kwarai Hajiya Allah ya bar xumunci, ya saka da alkhairi" tayi murmushi tace "Amin Alhaji" wani likita ne ya shigo ward din tare da nurse, yana ganin Abuturrab yace "Maa sha Allah, Allahu ya kara kiyayewa" Col yace "Xa mu iya tafiya ynxu ai" Likitan yace "Ehh toh, amma da sauran injections dinsa, xae karbi daya ynxu sae gobe da safe ya dawo" Col yace "Alryt" likitan ya juya ya fita, Col da Abban Ahmad suka bi bayansa, Hajiya Mariya ta d'an tabe baki ganin abinda yyi ma Abuturrab. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 91..... Ba su suka bar asibitin ba sai kusan karfe tara, su Umma suka wuce gida, ta so su biya can gidan don a daukar ma Noor da babies kaya amma Col yace gobe Hajiya Mariya xata je ta dauko masu, ya shiga motarsa Abuturrab ya shiga gaban motar shi ma, Noor ta shiga motar Hajiya Mariya tare da Mami dake rike da yaran, suna isa gida ya bude motar fuskar nan tasa bbu yabo bbu fallasa ya fita, Abuturrab ya bi sa da kallo kafin ya fito ya rufe motar, Mami ta fito da yaran, Hajiya Mariya ma ta fito ta karbi daya a hannunta, tuni Abuturrab ya nufi balcony, Noor ta bi sa da kallo, dafa ta Hajiya Mariya tayi sai taji tausayinta ganin tun daxu take mata magana amma bata san tana yi ba, ta kama hannunta suka nufi cikin gidan, ba karamin farin ciki su Ramla da Khaleesat suka yi ganinta da suka yi ba, har hakan ya bata mamaki sosai, amma ta fi xaton sbda yaran da suka gani ne, Hajiya Mariya ta wuce dakin Mami da ita ta kwantar da yaron hannunta ganin bata xauna ba tace "Toh xauna mana Noor" xata xauna kasa ta nuna mata gefen gado tace "Xauna a nan" ba musu ta xauna gefen gadon, Mami ta shigo dakin ta ajiye yaron hannunta gefen dan uwansa snn ta fita Hajiya Mariya ta kashe Ac dake kunne ta bi bayanta, bin dakin Noor ta dinga yi da kallo ban da kamshin turaren wuta me dadi bbu abinda ke tashi, ko ina na dakin fes fes, bude kofa aka yi ta daga kai suka yi ido hudu da fatima, gabanta yyi mugun faduwa, tare suka shigo da Ilham da ta nufo gadon da gudu tace "Woawww, twins for ya Abuu...." Daga haka ta dau Hussain ta manna masa kiss ta rungumesa cike da farin ciki tana kallon fuskarsa tace "He is sooo cute...." Kallon Noor tayi tace "Ya Abuu missed you all...." Noor ta d'an kirkiri murmushi sai dai gaba daya hankalinta na kan tunanin me fatima ke yi gidan, yaushe ma ta xo gidan, Ilham ta mika ma Fatima dake tsaye yaron ta dau dan uwansa shi ma ta manna masa kiss tace "Little angel, welcm to d world, am assuring you papa Love's you sooo much" Fatima ta ajiye yaron hannunta tace "Allah ya raya" daga haka ta juya ta fita dakin, Noor ta bi ta da wani kallo, Hajiya Mariya ce ta shigo da abinci dakin, da kyar ta kora ilham dake jin kmr ta hadiye kyawawan yaran, ta xuba ma Noor tuwon tace "To sakko ki ci Daughter" a hankali ta sauko kasa kan rug, duk da yunwar da take ji, ji tayi gaba daya abincin bai ranta, fatima dai tayi mugun tsaya mata a rai, haka Hajiya Mariya ta dinga forcing dinta tana tura abinci har ta ci da yawa, ta hado mata tea shi ma ta shanye snn ta kwashe kwanukan ta fita, Mami ta shigo dakin tace "Kin yi wanka kuwa?" Kai ta gyada mata tace "Nayi" Mami tace "Yaran fah?" Tace "Umma tayi masu" fita Mami tayi ta je dakinsu ilham ta dauko mata riga me kauri ta kawo ta bata tace "Tashi ki canja sai ki kwanta ki huta kin ji" Noor tace "Toh" Mami ta juyo ta fita, mikewa tayi ta canxa kayan snn ta kwanta kan gadon a hankali duk jikinta a sanyaye, can ta yamutsa fuska jin cikinta na d'an ciwo, ta koma kusa da yaranta dake ta bacci tana kallonsu, ji tayi duk duniya bbu wanda take so fiye da su, Abuturrab ya fado mata ta d'an turo baki ta kwanta kusa da su hade da lumshe ido. Hajiya Mariya na fita dama bedroom din Abuturrab ta shiga, jin yana wanka ta nemi gefen gado ta xauna, har dai ya fito bayan kusan minti ashirin, ganinta xaune ya nufo ta a hankali yace "Mum" tayi murmushi tace "Duk Samha ake ma wnn wankan Aliyu?" Bai ce komai ba ya xauna gefen gado yana goge gashinsa da karamin towel, ta kafa masa ido, can tace "Aliyu ban ji ka ce ma Samha komai ba, me hakan ke nufi?" Ba tare da ya kalleta ba yace "Mun gaisa ai mum, tun a can gidan" Shiru tayi kafin tace "Toh shknn" ta mike ta nufi kofa ya bi ta da ido. Tun Noor na daure ciwon da cikinta ke mata har ta kasa dauriyar kuma wajajen karfe daya da wani abu, sai juye juye take ga Hussain sai mutsu mutsu shi ma yake kusa da ita, Hajiya Mariya kuma na ta daya side din tare da Hassan, kuka Hussain ya tsala, Hajiya Mariya ta mike xaune ta kunna wutan dakin ta daukosa, ganin yunwa yake ji ta taba Noor da ta juya masu baya tace "Daughter tashi kiyi breastfeeding dinsa, he is hungry" da kyar ta mike xaune, Hajiya Mariya ta xagayo ta daura mata yaron kan kafarta jin Hassan ya fara taya d'an uwan nasa kuka ta xaga ta daukesa shi ma, Noor ta sauke rigarta, yaron na fara shan abincin ta ja baya da sauri jin wani ciwo da yafi Cramps axaba a kasan cikinta, yaron ya tsala ihu, Hajiya Mariya tace "Ya aka yi?" Cikin rawar murya tace "Mumy cikina ke ciwo" Hajiya Mariya tace "Ciki kuma? Tun yaushe?" Da kyar tace "Tun daxu" lkci daya hawaye ya shiga sakko mata, tun fara kukan Hussain Abuturrab dake xaune kan darduma ya dinga kallon kofa, jin d'an uwansa ma ya dauka sai ya kasa daurewa ya mike ya nufi kofa, kasa fita yyi can dai ya koma ya xauna yana jin yanda yaran ke tsala ihu, Duk ynda Hajiya Mariya ta so ta lallashesu kin hakura suka yi, Mami da taji kukan ita ma ta fito daga part din Col ta shigo dakin, tace "Me ya samesu Mariya, sun ki karban maman ne" Hajiya Mariya tace "Wai cikinta ke ciwo Mami, gashi bbu feeding bottles bare a ba su ko ruwa ne" Mami dake kallon Noor da ta kife kanta da gado tace "Subhanallah, bari in masa magana toh" a bakin kofa suka kusa cin karo da Abuturrab da dauriyarsa ya kare, ya ja baya da sauri yana d'an kame kame, tabe baki tayi tace "Toh shigo" yyi murmushi yana shafa kai ya bi bayanta suka shiga dakin, idonsa ya sauka kan Noor da ta kife kanta har lkcn, kallonta ya dinga yi har ya karaso cikin dakin, Hajiya Mariya tace "Cikinta ke ciwo Aliyu, ko akwai abinda xa ayi mata?" Shiru yyi yana kallonta, Mami tace "Ko a tafi asibiti?" Ya girgixa kai yace "Noo, it's normal Mami" hararansa tayi tace "Na fi ka sani ai likita" murmushi yyi yace "Akwae alluran paracetamol bari in dauko...." Daga haka ya fita, Mami ta kalli Noor tace "Tashi ki bi sa kin ji, Allah ya sauwake" mikewa tayi da kyar tana dingishi ta fita daga dakin, kasa shiga dakin nasa tayi ta duka nn bakin kofa hawaye na sakko mata, yana bude kofar ta mike da sauri ya kusa cin karo da ita, ya kalli kofar dakin Mami kafin ya jawo ta cikin dakin ya kulle kofarsa, kan gado ya tafi da ita, ya sa ta xauna yana kallonta, ta ki yrda su hada ido, sai hawaye take, a hankali ya sauke rigar jikinta yyi mata alluran, ganin kukan da take ya jawota jikinsa ya lumshe ido, Lamo tayi tana shakar dad'da'dan kamshinsa, tana kuma jin yanda xuciyarsa ke bugawa, murya can kasa taji yace "I...i..." Sai kuma yyi shiru, ta lumshe ido jin jikinsa da dumi sosai, sun fi minti goma a haka ya janyeta a hankali ya mike ta bi sa da kallo har ya shiga bathroom, ba a dau lkci ba ya fito rike da bowl din ruwan dumi da karamin towel, kwantar da ita yyi ya matse ruwan towel din bayan ya daura kan abdomen dinta yana d'an danna mata, mikewa tayi jin xafi ta bata fuska xata yi kuka, ya mayar da ita ya kwantar, a hankali ya dinga yi mata har ruwan ya salance snn ya kai bathroom ya fito tana kallonsa ya fita dakin, kitchen ya sauka ya bude fridge ya dau lime biyu ya xuba ruwan xafi a cup ya matse lime din ciki snn ya koma daki, da kansa ya dinga bata ruwan lime din har ta shanye ya ajiye cup din, hada ido suka yi tayi saurin sunkuyar da kanta, ya jawota jikinsa a hankali yace "How are you feeling now?" Lumshe ido tayi tace "Fine" bai kuma ce mata komai ba, suna nn a haka har agogo yyi stuck din karfe biyu, murya can kasa taji yace "Thanks for the babies Samha" bata ce komai ba, ya dago kanta yana kallon kwayar idonta ta kauda kanta, ya kamo hannunta yace "Why did you choose to leave Samha, you've caused me so much pains" Shiru yyi, ta koma baya a hankali tace "The babies...." Sai a snn ya kula har lkcn fa babies din sun ki hakura, ya mike ya fita, yana shiga dakin Mami tace "Ya jikin nata?" Yace "Da sauki Mami, bari a kai mata su xata iya basu abincin" Daga haka ya karbi na hannun Hajiya Mariya tace "Kai, wnn yara ba dai fitina ba kamar ubansu...." yar dariya yyi yace "Ke dai kawai don sun hanaki bacci ne mum, sae ma sun koma gun ki gaba daya" Dariyar tayi ita ma tace "Sae in xane su abu d'an sauki" yace "Toh baxa su ba, sai in kai su gun Yakumbo" yana magana ne yana kallon Mami da taki kallonsa ta mika masa Hussain ya fita da su yana murmushi, Hassan ya daura mata a kafa ya xauna yana lallashin dayan yana kallon ynda take basa abincin, bata ji ciwon kamar daxu ba, sai da yaran suka yi bacci duka snn ta kwanta, nn da nn bacci ya dauketa ita ma kmr xata shige jikinsu, ya jima xaune yana kallonsu, can ya d'a yi murmushi ya lumshe ido ya bude, ya hau gadon ya kwanta shi ma. Da Asuba yana dawowa daga masallaci ya tsaya bakin gado yana kallon irin kwanciyar da tayi da yaran kamar xa a kwace mata su, ya girgixa kai ya fita ya shiga dakin Mami, Hajiya Mariya na xaune kan darduma ya dau wayarta ys fita, hotuna ya dinga daukarsu ganin ta bude ido a hankali ya juya da sauri kmr yaran kadai yake dauka, sauka tayi daga kan gadon ta nufi bayi, yace "Kar kiyi amfani da ruwan sanyi" kallonsa tayi ta dauke kai ta shiga bayin, ya bi bayanta, brush dinsa ta dauka ya karasa ciki ya tara mata ruwan xafi ya tsirka snn ya fita, tana fitowa taga dakin wayam bbu yaran, kalle kalle ta fara yi, can ta nufi kofa da sauri suka kusa cin karo ta koma baya tace "Ban ga yaran ba kuma...." Kallon gadon yyi da mamaki fuskarsa yace "Toh ina suke?" Bata kuma saurarensa ba ta nufi kofa da sauri, ya rikota yace "Ina xa ki?" Kamar me shirin kuka tana kalle kalle tace "Xan je in duba su" yace "A ina" bata kuma saurarensa ba ta kwace kanta xata fita ya jawota jikinsa yana d'an murmushi yace "A gidan nan yaran ki xa su bata Wife? Na lura baki da kara, Mami ta daukesu xa a masu wanka toh..." Shiru tayi bata ce komai ba. Ya xaunar da ita gefen gado ya xauna yace "How did you feel rashin ganinsu just for some few minutes, dubi ynda kika hargitse, me yasa baki yi tunanin halin da ni na shiga ba all this while Samha, why did you choose to cause me so much pains??" Cikin raunin muryabm yake magana, ita dai bata bari sun hada ido ba, ya kamo hannunta ya kai kirjinsa a hankali yace "Feel it Samha..." Tana jin irin yanda xuciyarsa ke bugawa da sauri, a hankali yace "It's still not healed Samha, what have i done to deserve this from you?" Jin tayi shiru ya dago kanta a hankali yace "Talk to me Samha" still ta ki cewa komai, can ta sauke idonta a hankali tace "Nima ban sani ba" shiru yyi yana kallon fuskarta, matsawa tayi daga kusa da shi da damuwa tace "They are crying ko ruwan da xafi" wani kallo yyi mata yace "Ko xaki je ki duba?" Ta kallesa tace "A'a kai kaje, ni baxan iya ba" yace "Ashe ba son su kike ba" kamar xata yi kuka tace "Toh ka raka ni don Allah" ya mike yace "Toh mu je" tashi tayi da sauri ta bi bayansa, Mami ce ke ma Hussain wanka, Hajiya Mariya na rike da dayan dake tsala ihu shima jin d'an uwansa na kuka, Durkusawa Noor tayi kusa da Mami kanta a kasa tace "Ina kwana..." Mami tace "Lafiya lau, tashi a sanyi kin ji" murmushi kawai tayi ta kalli Hajiya Mariya ta gaisheta, ita ma ta amsa tana murmushi tace "Toh tashi mana" shi dai Abuturrab kallonta kawai yake, a hankali ta kai hannunta cikin ruwan kan idon Mami da Hajiya Mariya, Abuturrab ya juya da sauri kar yyi dariyar dake cin sa, Hajiya Mariya ta bude baki tace "Lallai Samha ruwan kike dubawa ko da xafi" kunya taji sosai ta kasa xaune waje daya tace "A'a mum, shine yace min in duba..." Mami da Hajiya Mariya suka kallesa a tare, ya juyo da sauri yana kallonta ya xaro ido yace "Ni?" Ta turo baki tace "Eh" *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 92___93 Dariya Hajiya Mariya tayi tace "To basa shi yyi masa wankan yaya" Mami kam murmushi kawai tayi tace "Da shi ma na k'ona sa yana jariri ae" fita Abuturrab yyi yana dariya, Noor ta mike ta bi bayansa, Hajiya Mariya ta rike haba tace "Ikon Allah, kin ga yaran yanxu koh?" Mami tayi murmushi tace "Su xo su tattara ma su bar min gida na sai ki je ki xauna da su, bn yrda da shirun nn na Col ba" Hajiya Mariya ta xauna tace "Wllh nima haka yaya, ba a banxa ba bin mu da ido da yake ya ki cewa komai Allah kadai yasan abinda yake kintsawa a xuciyarsa" Mami ta tabe baki tace "Kar ma yayarsa ta fado gidan, bn fiye son magana ba you know, snn ita ma yarinyar she is nt safe here....." Tabe baki Hajiya Mariya tayi tace "Bbu inda xa su yaya gwara ayi ta ta kare, ina ce ae yafi kowa shiga rudanin halin da Aliyu ya shiga don ma yana boyewa, i knw baxae so abinda xae kara taba ma d'an sa xuciya ba, bar sa ya gama shirunsa da kansa xae dawo yyi mana magana har ma ya bada ragon suna biyu" murmushi Mami tayi bata ce komai ba, Hajiya Mariya tace "Bari ma gari ya waye mu kira Hajiyar gombe, sae a kira kanwar babanta dake maraba ita ma a sanar da ita" Mami tace "Toh ni dai ki dau makulli ki tafi ki dauko ma yaran kayan da kika ce ke gidan ki, bbu kayan da xa su sa fa" Hajiya Mariya tace "Toh bari in kira yaran su rike maki wnn dake taya d'an uwansa kuka" daga haka ta ajiyesa ta fita suka dawo tare da fatima ta dau hassan, Hajiya Mariya ta dau makullin mota ta fita, Abuturrab na shiga bedroom dinsa Noor ta shigo ita ma, ya kulle kofar ya jawota jikinsa yace "Me nayi maki xa ki min irin wnn sharrin haka?" Ta hararesa tace "Toh ae baka ce min xa su gane ba idan na taba ruwan" kallonta ya tsaya yi, can ya lumshe ido ya rungumeta a hankali yace "I missed you Samha, kar ki sake bari na don Allah" lumshe ido ita ma tayi don tasan tayi kewarsa fiye da ynda take tunani, murya can kasa yace "Tell me how you felt when giving birth to our babies" sae da gabanta ya fadi tunowa da irin wahalar da tayi two days back, ta fashe da kuka ba hawaye tace "Ni baxan sake haihuwa ba, bana so" ya wara ido yace "Har ina cewa xa mu bar ma mum dinki wa enan tunda she is lonely without you sai ki sake haifa mana wasu yan biyun?" Da sauri ta dago tace "Da gaske?" Yace "Eh mana" a hankali tace "Toh a bata, xan haifa wasu" kamar warce ta tuno abu kuma tace "Nooo, my babies are muslims" ita kanta bata san lkcn da ta fadi hakan ba, ya dago kanta da sauri, ya xaunar da ita gefen gado yace "Really wife?" Sauke idonta kasa tayi, ya ji dadin furucinta har cikin ransa yace "So will der mother be one day" ta d'an kallesa, sae dai bata ce komai ba, yace "Toh wani sunan xa mu sa ma babies din?" Ta buda hannu alamar bata sani ba, ya kafa mata manyan idanuwansa. A bathroom din Abuturrab Hajiya Mariya ta taimaka ma Noor tayi wanka, suna fitowa ta sa ta shirya cikin sabbin riga da skirt na Ramla ko taba sa su bata yi ba, nn ta nuna mata lallausan rug dake shimfide a dakin da aka tula mata kayan breakfast, tun daga kan shayi da bread, kunu, wainar shinkafa, pepper soup din naman rago da ya ji yaji, sai tuwon masara da aka yi mata duk ita kadai, kuma ba wai da yawa ba, ko wanne dai-dai dai-dai aka yi sa, Abuturrab ne ya shigo dakin bayan fitar small mum dinsa, ya xauna kan rug din yana kallonta don ba karamin kyau tayi ba duk da bbu make up fuskarta, tayi haske haske sosai, yace "Kinyi kyau mumyn twins" bata ce komai ba, ya kai hannunsa kirjinta ganin ynda suka cicciko yace "For only our babies yanxu koh?" Buge hannunsa tayi, yyi dariya, ita kam murmushi tayi ta shiga hada tea, ya gyara xama yace "Shud i join dear?" Kallonsa tayi ta gyada masa kai, nn ya hada masu shayin su biyu, har ya mance yaushe rabon ya bude ciki haka ya ci abinci, ita kanta tasan ta jima bata ci abinci kmr yau ba, ya dawo kusa da ita ya rungumeta ya lumshe ido cikin sanyin murya yace "Ina son ki Samha...." Bakinta ta kai kunnensa a hankali tace "No more Samha, it's Noor... Noor Al-Hudah" kallon fuskarta yyi dai dai lkcn da aka bude kofar dakin ya janye jikinsa da sauri, fatima ta shigo rike da Hassan ta karasa kusa da shi ta mika masa, karban yaron yyi, Noor dama kallo daya tayi mata ta dauke kai, fatima ta juya ta fita, kasa kallon Noor yyi ya buge da kallon yaron dake ta mutsu mutsu da baki yana neman abinci, sai ga ta ta kuma dawowa da dayan shi ma ta mika masa ta fita, mikewa Noor tayi ta haye kan gado, ya bi ta da kallon gefen ido, jin yaran xa su fara kuka ya mike ya isa kan gadon ya xauna kusa da ita a hankali yace "Wife they are hungry" jin bata ce komai ba ya bude xip din rigarta, ta mike a d'an fusace, suna hada ido ta kasa cewa komai, ya sauke rigar kasa yana kallon kwayar idonta, a hankali ta shiga breastfeeding yaron da ya daura mata a kafa yana rike da dan uwansa, bayan minti sha biyar Hajiya Mariya ta shigo dakin tana tsaye daga bakin kofa tace "Aliyu idan kun gama ku je can gun Abban ku da yaran ku gaida sa" daga haka ta fita, haka kawai yaji gabansa na faduwa, Hijab din Ramla Noor ta sa, shi ya rike duk yaran biyu, yana gaba tana biye da shi har suka isa part din Abba, yana xaune hannunsa rike da newspaper idonsa sanye da Glass, kallo daya yyi masu ya ci gaba da karatun da yake, Abuturrab ya karasa kansa a kasa ya mika masa yaran, d'an jim yyi kafin ya ajiye takardan hannunsa ya karbesu gaba daya, ita kam Noor k'asan parlorn ta nemi waje ta xauna, ya kalleta ya nuna mata kujera, sunkuyar da kai tayi bata tashi ba yace "Xauna a sama" bata tashi ba still har sai da ya maimaita snn ta mike ta xauna, Abuturrab ya xauna nn kasa kusa da shi cikin sanyin murya yace "Good morning Abba" ba tare da Abba ya kallesa ba bbu yabo bbu fallasa yace "Morning!" Noor ma ta gaishesa kanta a kasa, ya kalleta yace "Morning, ya jiki" tace "Da sauki" kallon babies din hannunsa yyi, lkci daya yyi masu addu'a gaba daya ya mika ma ubansu, Abuturrab ya karbesu gaba daya, Abba ya jawo takardarsa ya ci gaba da karatun da yake, Hajiya Mariya ce ta shigo parlon da sallama, ganin ynda suke xaune shiru, shi kuma yana ta karatunsa ta kalli Noor tace "Tashi ki je Mami na kiran ki kin ji" kallon Abba tayi ta mike a hankali tace "Sai anjima" yace "Alryt" daga haka ta fita, Hajiya Mariya ta d'an tabe baki tace "Col tun asuba baka gama da jaridar nn ba" bai ko kalleta ba, Abuturrab ya mike yace "Sai anjima Abba" Ba tare da ya dago ba still yace "Ohk" Hajiya Mariya ta karbi yaran hannunsa tace "Ka karbi car key gun Mami ka jira ni xa mu fita" yace "to" daga haka ya fita duk jikinsa a sanyaye, Hajiya Mariya ta kuma kyabe baki ta karasa gun Col tace "Toh Abban Abuturrab Atm card xaka bamu mu je siyo ma jikokin ka kaya, bbu komai nasu a gidan nn" tana magana ne tana kallonsa, can ya dago ya kalleta yace "Ni xan bada Atm card?" Tace "Kwarai kuwa Sir, idan baka bayar ba waye xai bada Col" ya girgixa kai yace "Ki je dai ki karbi na uwarsa, bn yi budgeting siyan kayan yara ba wnn watan" dariya ma ya bata, ta ajiye yaran gefensa tace "Suna dai jin ka kar wataran su ce basa yi da kai kaji haushi, kuma kaya ne dai sae granny ya siya masu" daga haka ta nufi gun da ya ajiye makullin mota don ta hango Atm card din ta dauka tayi hanyar kofa ya bi ta da kallo har ta fita, can ya kalli yaran dake ajiye gefensa, ni dai har na bar dakin da takardata da biro bai daina kallon cute angels din gefensa ba. Bayan kusan awa daya Noor na kwance dakin Mami, sai dai gaba daya hankalinta bai jikinta don bata san inda yaran suke ba, gashi ta kasa tambaya, Ramla dai na ta gyaran press don a xuba kayan babies idan su Hajiya Mariya suka dawo, Mami na taimaka mata, Abba ne yyi sallama bakin kofa, Mami ta amsa sallamar ta karasa kofar da mamaki don ba haka nn yake tahowa bangarenta ba, bude kofar tayi ta gansa tsaye da yan biyu hannunsa yace "A basu abinci" karban yaran tayi tana kallon yanda suka yi da baki wai yunwa, tayi murmushi ya juya ya bar gun, ta shigo ciki ta ajiye su gefen Uwarsu tace "Tashi ki ba basu abinci Daughter" mikewa xaune Noor tayi tana kallonsu har bata san lkcn da tayi murmushi ba. Karfe sha daya na safiyar ranan Ummi ta iso gidan, ba karamin farin ciki tayi ba ganin twins din, ta rungume Noor da ta kasa kallonta tace "Samha kin bamu wahala da yawa" ita dai Noor bata ce komai ba, kaya ba kadan ba ita ma ta taho ma da twins, ganin bata ga Abuturrab ba tace "Ina Aliyun kuwa?" Mami tace "Sun fita da Mariya" Ummi tace "No more sickness knn koh" Mami tayi murmushi bata ce komai ba, Fatima ta shigo tare da su Ilham ta gaida Umminta suka fita, Ummi bata yi minti sha biyar gidan ba Umma da su Maryam da farida suka shigo, Mami taji dadin ganinsu ta tarbesu da fara'a suka shigo har bedroom ganin Noor, ba kaya na wasa ba suma suka taho ma da yan biyu, Mami tace "Amma ya ku ka gane gidan?" Umma tace "Ahmad ne ya kawo mu yana waje" Mami tace "Gashi Abuturrab din sun fita daxu wllh" bata rufe baki ba sai ga shi sun shigo da Hajiya Mariya, kansa a kasa duk ya gaida su, Ummi dai sai kallonsa take kamar tayi dariya ganin ynda yake sinne kai, a xuciyarta kuwa mamaki take duk irin gata irin tasa ya gwammace yyi ta wahala a kan so, Mami tace "Wai kun hadu da Ahmad?" Yace "Eh tare muka shigo yana parlor, na xo gaishesu ne" Mami tace "Ohk, kace ma su Ilham su kai masa ruwa" juyawa yyi ya fita, Noor dai duk a takure take a dakin, Mami na lura da ita tace "Ki je can dakin ki kwanta kin ji" a hankali tace "Toh" kallon yaran tayi ta mike ta fita, tunani ta dinga yi ynxu fa da xata fita gate bai fi tayi taku kadan ba xata isa gidansu, taga mumynta ta ga Abbanta, hawaye ne ya cika idonta tunanin hakan da tayi, ta shiga dakin Abuturrab a sanyaye ta kwanta. Karfe daya da kusan rabi Anty Maryam ta iso gidan, uhm duk ta fi kowa murnar ganin 'yar ta, duk ta rasa inda xata sa ta, ko ta kan yan biyu bata bi ba, Hajiya Mariya dai sai kallonsu take da tausayi haka ma Ummi, Noor na jikinta tace "Anty me yasa baki xo da Ihsan ba" Anty Maryam tace "Xa a kawo su daughter" can a hankali Noor tace "Anty baki tambayi babies dina ba" xaro ido Anty Maryam tayi haka ma Ummi, Hajiya Mariya tayi murmushi tana gyada kai, Anty Maryam ta ja hancinta tace "Amma baki da kunya daughter" shiru Noor tayi tana kallonta, can tayi murmushi ta boye fuskarta jikinta. Sai kusan la'asar Ummi ta bar gidan, ta so su koma da Fatima don next week xa su yi resume Mami tace ta bari sai anyi suna, su Umma dama tun biyu Abuturrab ya maida su gida don Ahmad ya wuce. Noor da dakin Abuturrab da Anty Maryam bayan tafiyar Ummi, Mami kuma na yi ma yara wanka, Anty Maryam tace "Kin san me Samha" girgixa kai tayi tace "Anty Noor xaki ce min ynxu" Anty Maryam tace "Noor kuma?" Ta gyada kai tace "Um haka su Umma ke kirana" Anty Maryam tace "Sbda me?" Murmushi tayi tace "Sbda am now a muslim" Anty Maryam ta buda ido tace "Kai daughter" tace "Wllh Anty" shiru Anty Maryam tayi tana kallonta can a hankali tace "Toh a wani dalilin kika yrda kika yi converting, in ji ba don Aliyu ba, ba kuma don yaran ki ba?" Girgixa kai Noor tayi tace "A'a, ai lkcn ban haife su ba, har ynxu kuma bbu wanda yasan nayi converting banda su Umma da kika gani daxu" Anty Maryam tace "To su suka ce kiyi converting din?" Tace "A'a i have my reasons" Anty Maryam tace "Toh ko xa ki iya gaya min reasons din" tana son sanin dalilin conversion din nata ne don bata son ya kasance don wani tayi hakan, Noor ta d'an yi murmushi nan ta shiga ba ma Aunt din tata dalilanta na komawa musulunci kmr yanda ta fadi ma Umma, banda Murmushi bbu abinda Anty Maryam take, can ta rungumeta tace "That's it daughter, gwara da kika fahimce hakan da kanki, Muslims are always their brother's keeper, infact ba ma brothers dinsu kadai ba, har wanda addininsu ya sha bam bam in most cases, am happy for you dear, Allah ubangiji ya sa Abbanki ma ya gano hakan da wuri daughter" a hankali Noor tace "Hadda Ummata" murmushi Anty Maryam tayi ta shafa kanta a xuciyarta kuwa cewa tayi da kamar wuya, a fili kuwa tace "Toh Allah ubangiji yasa hakan, na kira Abbanki nace you re back with ur babies, he was very happy, yace anjima da daddare kila ya shigo" Noor da ta ji wani mugun dadi har ranta tace "Anty da gaske xai xo?" Anty Maryam tace "Yace kila" ta girgixa kai tace "Noo plss ya xo don Allah ina son in gansa" Anty Maryam tace "Toh xai xo idan Allah ya yrda, one more thing daughter" Noor ta kalleta tana jiran jin me xata ce, Anty Maryam ta dafata tana kallonta tace "Ke bafulatana ce gaba da baya, a al'adar fulani kuma an san mu da kunya da kauda kai, mijin ki ma bafulatani ne gabansa da baya, kar kuma ki mance gidan surkan ki kike yanxu daughter, abinda nake so da ke bana son ki sake taba yaran nn sai an daukesu an baki su, ko kuma anyi insisting ki dauke su, na lura shegen son yara ke gare ki, kuma ban yi mamaki da yanda kika fito da hakan baro baro ba don haka mamarki ma take" ita dai Noor kallonta kawai take, ta ci gaba tace "Duk kukan da xa su yi idan ba gun ki suke ba bbu ruwanki kin ji daughter, kar a dinga ganin rashin kunyar ki" Sunkuyar da kai tayi cikin sanyin murya tace "Toh" Anty Maryam tayi murmushi ta ja hancinta tace "Yauwa maman biyu" murmushi ita ma tayi ta boye fuskarta jikinta. Bayan Magrib Noor na xaune dakin ta sa pepper soup din da wata k'awar Mami ta kawo mata gaba ta kasa ci sbda yajin da yyi mata yawa, Hajiya Mariya ma na dakin da Mami suna jera uban kayan twins dake xube kasa kamar baxa su girma ba don kayan da Hajiya Mariya ta siyo masu tare da Abuturrab ma yawan su ba a cewa komai, ta kashe ma Col yafi dubu dari biyu duk a kayan yara, shi dai bai ce mata komai ba ta ajiye atm ta kara gaba, lkci lkci Noor kan kalli yaran da suke kwance kan gado sai motsi suke da ta kallesu kuma maganganun da Anty Maryam tayi mata sai ya fado mata, hakan yasa har suka fara kuka bata yi yunkurin daukarsu ba, sai Hajiya Mariya ce tace "Jariran nn sun cika son hannu naga alama" daga haka ta nufe su, Anty Maryam ce ta shigo dakin da sallama tayi masu sannu da aiki, tana kallon Noor tace "Har ynxu baki gama ba, to rufe ki xi ku gaisa da Abbanki" mikewa tayi da sauri tace "Abbana" Bayi ta shiga da sauri ta wanke hannunta ta fito, ta nufi kofa, Mami da Hajiya Mariya suka bi ta da kallo cike da tausayinta, Anty Maryam kam murmushi tayi ta juya ta bi bayanta, Noor na sauka kasa taga Abbanta xaune parlorn, da Abuturrab da Col, ae bata san lkcn da ta taho da gudu ba ta fada jikinsa tace "Abbana!" murmushi yyi yana kallonta yace "Samantha...." Rungumesa tayi hawaye ya cika idonta tace "I missed you Abbana, i missed you" har lkcn yana murmushi yace "I missed you more daughter" hawaye na sakko mata tace "Abba Mumy fah?" Yace "She is home" tana goge hawayen da yaki tsaya mata tace "I wish i can see her" Abuturrab dai sai kallonsu yake, yaji wani iri har cikin ransa, Col ma dai kallonsu yake shi ma, Hajiya Mariya ce ta shigo parlon rike da Hussain, Ramla kuma na rike da Hassan suka nufo su, yana ganin haka ya janyeta jikinsa, Hajiya Mariya ta mika masa yaron tana murmushi ya karbesa, Ramla ta mika masa dayan ma, kallon yaran kawai yake, can yyi murmushi ya kalli Noor yace "Are you sure babies din ki ne wnn daughter" turo baki tayi tace "Nawa ne fa Abba" ya girgixa kai yace "A'a ba naki bane" tace "Abba wllh nawa ne" yace "Noo" kamar xata yi kuka tace "Da gaske Abba nawa ne" ya ja hancinta yace "You are nt saying the truth" kamar xata yi kuka tace "Am nt lying, they re my babies" yace "Hw will i believe they re urs, gashi ba su yi kama da ke ba?" juyawa Hajiya Mariya kar dariya ya subuce mata, Abuturrab ya sunkuyar da kansa yana murmushi, Hawaye har ya fara cika idonta ta kalli Abuturrab, Col ya d'an yi murmushi shi ma, kuka ta fara yi ta rufe kanta jikin Abbanta, Anty Maryam dai sai kallon ikon Allah take, Hajiya Mariya tace "Ki bar daddy daughter, yaran ki sun yi kama da ke kin ji" Murmushi kawai Abban nata ke yi ya kai bakinsa kunnenta yace "Yea, sun yi kama dake My daughter, they are beautiful just as you, i love them just as i love you...." A hankali ta dago kanta tana d'an murmushi tace "Thanks Abbana," yace "Yea my Samantha" turo baki tayi tace "Abba am nt Samantha any longer" ya d'an bude ido yace "Who are you then?" Lumshe ido tayi tace "Noor..." Yace "Ohh really? Noorul Islam?" Daga Abuturrab har Abbansa kallonsu kawai suke, ta girgixa kai tace "Rather, *Noorul Huda*" Gyada kai Abbanta ya dinga yi yace "Light of Guidance you mean" ta wara ido ta rungumesa tace "Yes Abba, i want to be just as my grandpa" Murmushi ya dinga yi yace "All the best daughter" Noor ji tayi kamar kada Abbanta ya tafi duk da ya kusa minti talatin a gidan, ana kiran isha yace xai wuce, Dad din Abuturrab ya rakasa suka fita. Abuturrab sai kallonta yake ganin ynda take hawaye, ta galla masa harara ta mike ta bar parlorn tana share hawayenta, mikewa yyi ya bi bayanta bedroom din Mami xata shiga ya jawota xuwa nasa bedroom din ya rufe kofa ta fashe da kuka, rungumeta yyi yace "Ae tun da kina nan kullum xai dinga xuwa fa wife" lamo tayi jikinsa tana sheshsheka, ya lumshe ido yace "Yaushe kika dawo Noor wife, you re getting me confused" bata ce komai ba, ya ja ta xuwa gefen gado ya xaunar da ita yace "Kin ji dear" tace "Ba ruwan ka" shiru yyi yana kallonta, can ya d'an yi murmushi yana kallon dogon hancinta yace "Ohk" hannu ya kai hancin nata yace "Ta nn kadai twins suka maki kara, ba don kuma nima nawa bashi da kyau ba.... Amma bakinsu, idonsu, fuskarsu, infact komai nasu nawa ne" yana magana ne yana mata wani irin kallo, ta tabe baki irin kan ka ake ji din nan, dariya yyi ya rungumeta yana kiss din wuyarta yace "There is always reason for everything baby" lumshe ido tayi bata ce komai ba. Haka Noor ta dinga samun kulawa yanda ya kamata gidansu Abuturrab, babu abinda aka raga mata ita da yaranta biyu, shi dai Col har lkcn an kasa gane inda ya dosa don haka yake bbu yabo bbu fallasa, ana gobe suna Anty Maryam ta dawo gidan da sassafe, irin shirye shiryen da ake yi gidan sai ka rantse biki xa ayi, bikin ma mai aji, da rana misalin karfe biyu Ahmad ya aiko da raguna biyu, hakan ya ba Abuturrab mamaki har su Mami, nan Mami ta kira Ummarsa tayi mata godiya sosai, a ranan da yamma Abban Noor shi ma ya aika nasa ragunan biyu, Abuturrab na waje tare da old time frnds dinsa da suka xo ganin babies kiran Sadeeq ya shigo wayarsa, ya dauka suka gaisa Sadeeq yace "Ya boys dina?" Abuturrab yace "Sunan nn, growing fast, suna kuma missing rugged dad nasu Sadeeq" Sadeeq yyi dariya yace "Awwwnn, am missing dem more, in'sha Allah gobe xan shigo Nigeria just because of them, xan ma transfer ynxu ka tashi ka shiga kasuwa ka samo masu biggest of rams biyu plss...." Abuturrab yace "Ohh i knw they will be grateful Abbakar, buh an siyo masu raguna da yawa, just get dem something different" Sadeeq yace "Alryt then, till i cum, a shafa min kansu, a kuma gaida min mai jego" Abuturrab yace "Alryt frnd, thanks much" karfe shidda na yamma Ummi ta iso a ranan, Mami ta ji dadin ganinta don abubuwa sun fara shan kansu, aiki yyi yawa sosai, lafiyayyen dinkin atamfar English biyu tayi ma Noor sai jewelries masu kyau, su Mami suka dinga godiya, ta bude jakarta ta fiddo wani box din earrings ta bude ta ciro dankunnen zinari me kyau a ciki ta mika ma Noor tace "Gashi daughter naki ne wnn" ta kalli su Mami dake kallonta da mamaki tayi dariya tace "A'a ba ni na siya mata ba, sadakinta ne dubu hamsin da Aliyu ya ban da dadewa, naga wnn xai fi dacewa shi yasa na siyo mata" Mami tayi murmushi tace "Allah sarki, to mun gode Hajiya, Allahu ya bar xumunci" ita ma tana murmushin tace "Amin" bayan Magrib aka shigo da babban cow gidan da kayan abinci me yawa, Abuturrab ya riga ya san Abbansa ne ya siya kuma hakan ne shi ya siya, sai bayan da ya bari ya tafi part dinsa snn ya bi sa, xaunawa yyi a kasa yana kallonsa a hankali yace "Abba Allah kara budi, mun gode sosai" Hade rai yyi yace "Godiya na me?" D'an murmushi Abuturrab yyi bai ce komai ba, Abba yace "Leave now before i kick you outttt" mikewa yyi yana murmushi ya fita daga dakin, Abba ya ciro wayarsa ya nemo number yayarsa, a hankali yyi dialing number tana dagawa tace "Ahmad" yayi kasa da kai yace "Na'am yaya kuna lafiya" tace "Toh lafiya lau kenan xa ace, ya gidan, da yara?" Yace "Alhmdllh" tace "Toh Allah yyi albarka, har yau Ali shiru ko Ahmad!" Shiru yyi don ko yaushe xai kirata sai tayi maganan Abuturrab, tace "Kana ji na Ahmad" yace "Ina ji yaya, Aliyu ya dawo" da karfi tace "Ya dawo??" Yace "Ehh" wani kabbara tayi tace "Yaushe?" Col yace "Kwanan nn" tace "Toh madallah, gari na wayewa xan dau hanyar kano idan Allah ya yrda," yace "Ba shi daya ya dawo ba yaya" ta tsuke fuska tace "Shi da wa?" Yace "Shi da yarinyar da yan biyu maza, gobe ne sunan yaran ma" bude baki tayi tace "Har da 'ya ya? Wato aurenta dai yyi koh Ahmad" yace "Ehh yaya" tace "Toh xa mu gani, ina nan xuwa jibi da sassafe in sha Allah ayi ta ta kare" daga haka ta katse wayar, ya mike ya isa window yana kallon waje ya rungume hannayensa. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 94..... A daren ranan Abuturrab ya ishi Noor ta fadi sunan da take son a sa ma babies din tace ita bata sani ba, ya langwabar da kai yace "You mean baki da sunan da kike so a ran ki?" Nan ma ta girgixa masa kai, murmushi yyi yace "Toh shknn" gun Maminsa ya tafi yyi shawara da ita sunan da yake son rada ma babies din tace Allah ya raya su amma ya samu Abbansa dai tukun, ko da ya sanar da Abbansa xai yi masa takwara girgixa kai yyi yace "A'a na yafe" Abuturrab yyi shiru yana kallonsa, can Abba yace "Yea sbda mahaifinta hakan baxai yiwu ba, ka rada masu wani sunan daban, there is next time" Daga haka Abba ya mike ya dau wayarsa dake ring ya nufi kofa, Abuturrab bai iya yace komai ba don shi ma da farko yyi wnn tunanin bai mata adalci ba idan yasa nasa mahaifin, an dai san baxai kama ya sa ma d'ansa David ba, Washegari da ya kama friday aka rada ma twins sunansu, Hassan ya ci sunan Ahmad d'an Umma, Hussain kuma aka rada masa Abbakar Sadeeq, ya ci sunan Sadeeq, don wa ennan mutanen ne Abuturrab bai jin xai iya mance su a rayuwa, duk da ba wai Ahmad ya taka wani rawa bane amma tunda har shi ya kuma hada sa da Noor dinsa baxai mance sa ba, wannan suna dai ya samu halartar mutane da dama har da abokan col, har hakan ya dinga ba Hajiya Mariya da Mami mamaki, idan ka ga Noor a wnn rana sai kayi xaton amarya ce tsabar kyau da haduwar da tayi, sosai Mami suka kashe kudi gun ganin sun fito da ita, irin yanda mutane daga nisa da kusa suka cika gidan Col bbu masaka tsinke abun ba a magana, da gani kasan Abuturrab ba karamin d'an gata bane ko daga kan cimar da aka yi domin sunan, ni kam nace to da an gaya maku baban nawa na wasa ne ko don kun gansa a banxa yana wantagalili a gombe da maraba? to dai tillon d'a ne ga Colonel guda, sake baki da idanuwa nayi ganin members na Khaleesat Haiydar Novels su Maman Shakur, Ummu ilham, chamo, Anty Fyn, Ashmaad, Fiddo s dangi, Mimic, Fa'ee, Zuhoorah, Ummu Zainab, Ummu Amana, Humainah, Jamila.... kaiiii ni kam ina xan iya lissafo su... zaxxaune na hangosu kan kujeru ko wannensu ya cakare cikin ankon da suka yi na wani ubansun lace kalan sea green sai head jaa, sai daukar ido suke, ga abinci kala kala an ajiye ma kowa a kan table din gabansa daga gefensu kuma tulin gifts din yan biyu da suka yi wrapping a wrapping paper iri daya ne, Hajiya Mariya da Anty Maryam suka dinga bi suna gaisawa da su, ni ko na rike baki nace "Ohhhh wa yaga gayyar sodi😜" don ni dai nasan banda phatiemarkh bbu warce na gayyata wnn sunan, ae fa ban sake bakin da na rike ba na hango wata tawagar guda na 'yan haske writers💡su ma suna xaxxaune nace "Toh fahhh" su Ummy Shatu ne, Fatyma Zahrah, sweet sis Asmy B Aliyu, Billy Galadanci, Mom Ihsaan, faxy, Safiyya Huguma, Ayusher, feedohm.... kai gaskiya suna da yawa, su ma sun cakare cikin ankonsu na holland da suka yi ko wannensu sanye da siririn glass na 'yan gayu su ma ga uban gifts dinsu ajiye a gefe, Ummi sai bi take tana gaisawa da su, cannnn cikin jama'ar asali da aka gayyata aka basu pass din shigowa gate din Colonel na hango Iqram Mujaheed tana ta rawan kan kwaso drinks da ruwa tana raba ma mutane uwa an sa ta, ita a dole k'anwar khaleesat Haiydar bakin nn yaki rufuwa, na kyabe baki nace wa yaga karere🙄, kai na bai gama daurewa ba sai da nasamu lbrin ae fa akwai wani canopy da aka kafa a waje na gayun😎 Khlst Hydr Nvls su ma sun sha anko cikin shadda fari tas irin na Abuturrab da Sadeeq dake bi yana gaisawa da su, nace cabdi abun na yi ne oo.... Noor kam duk wnn budurin da ake bata da walwala, da ta tuna Anty Maryam da yaranta kadai ne nata a gidan sai hawaye ya cika idonta, ko ba a fadi ma Anty Maryam ba tasan me ke damun yar tata, ita ma duk sai ta ji wani iri. A can gidan Mr David kuwa yau kwana biyu knn Rachael ke fama da ciwon kan dake sa ta fita hayyacinta idan ta fara shi, duk asibitin da xa su bbu sauki sai don kansa yake tafiya, da yake ta kwana biyu bata yi ciwon ba sai take jin sa kamar sabo, abincin da mai aikin gidan ta girka Mr David ya kai mata har daki, tana durkushe bakin gado Bible a kusa da ita, ta rataye rosary a wuya, ya ajiye xai fita, cikin sanyin murya tace "Yanxu da Samantha tana kusa dani ciwon nn baxae kada ni haka ba, for heaven sake sai yaushe 'ya ta zata dawo garen, yaushe ne wnn rana da xan ga samantha" tana magana ne zar tausayi idon nn cike da kwalla, ya dawo dakin ya xauna jin tausayin matar tasa, glass din idonsa ya cire yace "Ke ce Rachael fadan ki ya fi karfin ki, nasan Samantha na son xuwa gun ki amma tana tsoro" Kallonsa take tace "Ya baxa ta ji tsoro ba bayan ta cuce ni, haka kawai ta mayar da ni barren din karfi da yaji kamar ban taba haihuwa ba, yanxu sai dai in ga wasu da 'ya ya ni bani da, ta fiffita namiji a kai na" tana kai wa nn ta fashe da kuka sosai, shiru yyi yana kallonta, can yace "Yanxu da xa ki ga samantha tsakanin ki da Allah ya xa ki yi Rachael" mikewa tayi tana share hawayen idonta tace "I know it, nasani dama, David ka san inda Samantha take shi yasa baka damu ba, nasan kai da kanuwarka kun san komai, kun san inda 'ya ta take, munafurtata kawai kuke" ta fashe da matsanancin kuka tace "Me nayi maku David da xa ku bar ni da kadaicin 'ya ta haka, ita ma fa Maryam Uwa ce, idan yar ta tayi mata haka xata ji dadi, tsawon lkcn nn kun san inda ya ta take ku ka bar ni ina yawo duniya nemanta, what have i done to deserve dis" Girgixa kai yyi yace "Haukan ki ne yafi karfin ki shi yasa bbu wanda ya damu ya nuna maki yasan inda take, ina ce kwanaki cewa kika yi kasheta xaki yi da xata shigo hannun ki, toh ko nasan inda 'ya ta take wnn furucin naki xai sa in fito in gaya maki" a fusace tace "Kai baka san baraxana ba david, kaza ce da xan kasheta, ko wani ya dau min cikinta yyi wahala ya haifar min ita da xan kasheta" yace "Better, Samantha tana nn lfya kuma ita ma tana kewar ki tare da tagawayenta maxa" rikosa tayi a rikice tace "A ina take David?" Yace "Tana nn lafiya dai" ta fashe da kuka sosai tace "Amma kuma baxan ji inda take ba koh, sbda ni ba xuciya ce a kirjina ba koh, sbda ba ni na haifeta ba koh," xaunar da ita yyi gefen gado yace "You make me a promise that you will act smartly idan na kai ki inda samantha take, ki min alkawarin baxa ki yi abinda bai dace ba a can...." Share hawayen idonta ta shiga yi da sauri tace "Na ji David" yace "A'a ba kin ji ba, cewa nayi ki min alkawari" tace "Nayi alkawarin" yace "Good, ki ci abinci sai ki shirya in kai ki inda take" mikewa tayi da sauri tace "Am full, kuma a shirye nake dankwali kawai xan daura" duk ynda ya so ta ci abinci kin ci tayi, yace to ta jira a idar da magrib, ana idarwa kuwa suka bar gidan a motarsa suka taho gidansu Abuturrab, kallon gidan kawai take da shock, yace "Kin dai yi alkawari Rachael" daga haka ya fito ta bi bayansa da sauri, number Maryam ya kira yace mata yana waje ta fito, ba a dau lkci ba sai ga ta, ba karamin kidimewa tayi ba ganin Rachael, ita ko tana tsaye idon nn cike da hawaye, Maryam ta kasa cewa komai duk jikinta yyi sanyi, Mr David yace "Ki shiga da ita ciki ta ga Samantha" a hankali tace "Toh" daga haka ta shiga ciki Rachael ta bi bayanta, Mr David ya koma cikin motarsa, suna shigowa parlor Hajiya Mariya dake ta gyare gyare ta dinga kallonsu kuma ko ba a gaya mata ba ta san wacece don ta taba ganinta, xaunawa Rachael tayi tana kare ma parlon kallo, Anty Maryam na kallon Hajiya Mariya tace "Hajiya mahaifiyar Samha kenan" Hajiya Mariya tayi karfin halin ce mata sannu da xuwa, Anty Maryam kuma ta wuce sama, Abuturrab ne ya shigo parlorn tare da Sadeeq, still yyi yana kallon Rachael da mamaki, ita ko kallo daya tayi masa ta dauke kai, Sadeeq kansa sai da yayi jim ganinta, da kyar Abuturrab ya karasa parlorn ya xauna yace "Ina yini?" bata kallesa ba bare ta amsa gaisuwarsa, ya kalli Sadeeq da ya wuce sama abun sa, can ya mike ya bi bayansa, Noor da har ta fara baccin gajiya ta saka Hijab suka fito tare da Anty Maryam da ta dau Ahmad, Ilham kuma ta dau Abbakar, bata san dai da wanda xa su gaisa ba amma ta fara gajiya da fitowa, a corridor suka hadu da Abuturrab, ya gaida Anty Maryam tayi masa sannu da xuwa, kallon Noor da ta ki dago kanta yyi sai ma wucewa gaba da tayi ta bar su a gun. *Haske writers asso* Mumy's, Anty's, Uncles.... Lil Haiydar is grateful for the wishes, Allah bar xumunci.💝 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 95..... Anty Maryam tace "Did you greet her? I mean her mum?" Abuturrab ya gyada kai yace "Na gaishe ta" bata kuma cewa komai ba ta bi bayan Noor da har ta sauka kasa, a hankali Noor ke tafiya tana kallon wacce ke xaune kan kujera tayi backing dinta, haka kawai gabanta ya shiga faduwa sosai, can ta daga kai ta kalli Hajiya Mariya dake tsaye parlon, sunkuyar da kai tayi ta karaso cikin parlon, kasa motsi tayi inda take tsaye bayan sun yi ido hudu da mum dinta, ta rufe bakinta kar ta saki ihun dake shirin fitowa bakinta, lkci daya hawaye ya cika idonta, ta karasa da gudu ta fada jikinta ta rungumeta ta fashe da kuka sosai cikin rawar murya tace "Mumy..." Rachael dake ta mata wani kallo ta turata gefe tace "Ja can munafuka duk tsawon lkcn nn baki san inda nake bane xa ki fashe da kukan munafurci, ni kika so kashewa ko? Toh God of Abraham ya fi ki, ina nn ban mutu ba" sai kuma ta fashe da kuka sosai tace "Yanxu Rebecca namiji kika xaba a kai na koh? Kika dau namiji uba sbda hankalin ki ragagge ne koh Samantha?" Noor ta kuma fashewa da kuka sosai tace "Forgive me mum, don Allah ki yafe min" buga bakinta tayi tace "Shut up, in kin ga na yafe maki to Jehovah ma ya yafe maki ne, don ba ni kadai kika yaudara ba har shi" Anty Maryam dake tsaye kansu dai bata ce komai ba, a hankali ta jiye mata Ahmad dake hannunta a cinyarta, Rachael ta hadiya sauran fitinar dake shirin fitowa bakinta tana kallon yaron, Ilham ma dake tsaye gefe sai kallon ikon Allah take ta karaso ta ajiye mata Abbakar shi ma a jikinta, Rachael dai sai kallon kyawawan yaran take, tuni dama Maryam ta bar parlon sai Hajiya Mariya dake tsaye da ilham, can Rachael ta goge hawayen idonta tace "Eh toh da yake duk abinda jehovah ya rubuta sai ya faru, wnn abun da ya same ni rubutattce ne, kuma ni na gode ma Allah da na iya jure wnn bak'ar faith din" Daukar Ahmad tayi ta rufe ido tace "You are blessed in jesus name...." Hajiya Mariya ta yo waje da ido haka ma Ilham, ta ajiye yaron ta dau dan uwansa shi ma ta fadi masa haka, snn ta fara masu addu'a idonta rufe dai dai shigowar Col parlon, tsaye yyi yana kallonsu, can yyi murmushi yana gyada kai ya wuce sama, ita dai Noor na xaune gefe ta kasa dago kanta, Rachael tayi addu'a me isarta ta kare adduar da cewa "You are all covered with d blood of jesus my babies" snn ta bude idon ta hade rai tace "Tashi dauko mun kayansu mu wuce gida," Kallonta kawai Noor take ta kasa cewa komai, can ta juya a hankali kalli Hajiya Mariya dake ta kallon ikon Allah, tuni Rachael ta mike tana rike da yaran tace "Wai ba kya ji na ne" Noor kamar xata yi kuka tace "Mum...." dungurinta Rachael tayi tace "Baxa ki tashi ba sai na mare ki" Hajiya Mariya tace "Amma Madam kinga baxai yiwu su fita ba ynxu jego fa take, ina xa ku cikin sanyin nn" wani kallo ta watsa ma Hajiya Mariya tace "Sai aka ce maki a kafa muke? Wato ku kadai ne masu mota koh?" Daga haka ta kuma yi ma Noor tsawa tace "Tashi nace, ba ma sai kin dauko kaya ba ynxun nn sai david ya fita ya siyo masu" Ilham ta juya ta wuce sama don kiran Mami, Sai ga Mami da frnds dinta biyu da Ummi sun sauko parlon, Mami na kallonta tace "Ina yini" ba tare da Rachael ta kalleta ba tace "Lafiya qlau" Ae da ta sake yi ma Noor wani tsawa bata san lkcn da ta mike tsaye ba a tsorace, fuskarta a tsuke tace "Fita mu je nace ko nan din gidan uban ki ne" Frnd din Mami Hajiya Rahina dake tsaye tace "Amma kuma Madam ae gidan Uban yaran hannun ki ne" a dakile Rachael ta dinga kallonta tace "So? Idan gidan ubansu ne sai aka yi yaya? Ina ce ita ta haifesu?" Hajiya Rahina ta girgixa kai tace "A'a kmr ynda kika ce ta tashi ku tafi gidan ubanta, su ma sai ki bar su gidan ubansu" Tsaki Rachael ta ja tace "Toh baxa a bar su ba, abinda nake so ki gane a nn shine ae ba wani ya haifar mata su ba, ba uban ya haifesu ba" Hajiya Mariya tace "Amma kuma ai mijinta bai mata izinin tafiya ba naga" Rachael tace "Wani mijin, ni ban ma 'ya ta aure ba, kar wanda ya sake lakaba mata miji, duk da ma ni ynxu ba ta ita nake ba, albarkacin nonon da xata basu yasa ma ni xan tafi da ita yanxu, banda haka ni da ta bi ni da kar ta bi ni duk uwasu daya ubansu daya, yara ne dai suka xama dole in tafi da su don nawa ne, dama ance min duk 'ya yan da ban haifa ba ita xata haifar min su, ba don ita kadai Allah ya halicce ni ba," Ita dai Anty Maryam na sama tana jin hayaniyar Rachael ta kasa saukowa, ganin dai ta dage sai ta tafi da yara da Noor tayi karfin halin saukowa parlorn, da kyar tace "Sister Rachael bai kamata kice xa ki tafi da su ba, kin ga....." Wani tsawa Rachael tayi mata tace "Munafukaa, muna nn dake Allah xai mani sakayya, ba dai 'ya ta kika jefa a halaka ba har abada ni dake Maryam kuma ni ba yafewa xan yi ba, kika sake tsomo bakin ki nn kuma sai na baki mamaki, muguwa kawai" Mami dai sakin baki tayi tana kallon ikon Allah, Ummi da ta kasa cewa komai tun daxu tayi karfin halin cewa "Madam kiyi hakuri don Allah a xauna ayi magana ta fahimta" ta gefen ido Rachael ta kalleta tace "Ban san shi ba, fahimta dai koh? To ni bn san shi ba" Abba ne ya dawo parlon yace "Ku bar ta su tafi, you go with them...." Muryar Abuturrab suka ji yana saukowa daga stairs yace "Noo Abba.... they are nt going with my children" Noor ta juya tana kallonsa hawaye cike idonta, Rachael tayi wani shewa tana hararansa tace "Halan kai ka dau cikinsu ka haife su??? Ai idan kaga na fita bbu yaran nn yau toh a sume aka fitar da ni parlon nn, suman ma irin dogon nn da ban san waye a kai na ba, yau dai jikokina baxa su kwana gidan nn ba ko da ita bata yrda ta bi ni ba ta sha xaman ta, kuma daga nn church na nufa da yara a sa masu albarka kmr yanda kaga uwarsu tayi albarka har ta haife su" Mami sai kallon Abuturrab dake tahowa take, Sadeeq kam tsaye yyi sama ya rungume hannu yana kallonsu, Abuturrab ya karaso parlon ya girgixa kai yace "Sorry ni baxa ki fitar min da yara gidan nn ba, it's nt, nd wil never be possible" tana masa wani kallo tace "Then i will show you that it's very possible" Abba ya kallesa ya hade rai yace "Leave immediately now" ya girgixa kai yace "But she can't just leave with my children dad...." Wani tsawa Abba yyi masa yace "I said leave now" Rachael ta ja tsaki tana hararan Noor dake kuka sosai tace "Idan kin so ki biyo ni ko kar ki biyo ni, hakan baxae sa jikokina su yi starve ba, i will get them a better milk" daga haka ta nufi kofa tana wakan church, Sadeeq ya sakko da sauri yace "But Abba ina xata kai yaran mutane, she can't just..." Wani kallo Abba ya watsa masa shi ma yace "Leave too before i kick you out" Noor ta xube kan kujera ta fashe da kuka sosai, lumshe ido Abuturrab yyi maganganun Small mum dinsa da tayi masa da dadewa na yawo a kansa 'meye makomar kids din ka Aliyu??? kar ka manta ita xa kayi converting ba family dinta ba, sannan Kasan baxa ta taba rabuwa da family dinta ba, Aliyu keep everything aside and think reality, this is the biggest mistake you are to make in ur life' bude ido yyi ya juya a hankali yana kallon Small mum din tasa ya ga ita ma kallonsa take, Hajiya Rahina da kanta ya gama daurewa tace "A'a Col, gaskiya wnn ba magana bace ya xaka ce a bar ta ta tafi da su, kaji fa inda take cewa xata kai su ynxu wai church!" D'an murmushi yyi yace "Kin mance wanda ya k'i ji baxae k'i gani ba? Shi ya ji ya gani kuma xai iya, i just love her action, bbu kuma ynda xa' ayi a rabata da jikokinta kema kin sani, yes ta kai su duk inda xata kai su she have the right" Ummi da ranta ya gama baci tace "Noo Abban Aliyu, u re sounding Sarcastic" Col ya girgixa kai yace "Rather, i am absolutely right" daga haka ya juya ya bar parlon, wani kallon gefen ido Sadeeq ya bi sa da shi haka ma Hajiya Mariya dake ji kmr ta kwade sa, Mami kam tuni hawaye ya fara sakkowa idonta, shi dai Abuturrab ya kasa kallonta, tuni Rachael ta isa kofa xata fita suka kusa cin karo da Yakumbo da ta rafka uban sallama da kaya niki niki a kai" *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 96..... Yakumbo ta dire kayan dake daure kanta tana kallon yaran hannun Rachael da ke kkrin fita kofa tace "Ke ya haka, ina xaki kai 'ya yan mutane da magariba, wani gwanannen ne baxai shigo ba sai an fitar masa da 'ya yan waje cikin sanyin nn" ko kallonta Rachael bata yi ba ta fice daga parlon, Yakumbo ta juya tana kallon su Hajiya Mariya dake tsaye parlorn tace "Wace mahaukaciya ce kuma wnn? ko dai kurma ce" Hajiya Mariya tace "Sannu da xuwa Yakumbo, ba mahaukaciya bace, xuwa tayi ta tafi da yaran wai" Yakumbo ta d'an yo waje da ido tace "Ta tafi da su? Ina xata kai su" karasowa parlon tayi tana kallon Mami da ta kasa daina hawaye ta kuma kallon Hajiya Mariya tace "Ke wai me ke faruwa, Aliyun sake gudu yyi?" Bata rufe baki ba ta gansa tsaye kansa a kasa yana rungume da hannunsa, ta tafe hannu hade da kyabe baki tace "Ikon Allah, Ka gaji da guje gujen ka dawo kenan, ae dama duk wawan da ya bar gida da kafarsa to fa da kafafuwar nn xae dawo in da rai da lafiya, ni ba dan naka naka bane da na ja maka Allah ya isa a kan wahalhalun da ka saka k'anina Aliyu, uwar ka kam dama bakin ku daya da figaggiyar kanwarta...." Daga haka ta ja tsaki tace "Na xo ne dama ayi ta ta kare ina Ahmad din..." Daga haka ta dau hanyar stairs, Rachael na fita gate Mr David ya fito daga mota da sauri yana kallonta da mamaki yace "Rachael meye haka, ina xa ki kai yaran?" Wani kallo ta jefa masa tace "Ina xan kai su kamar yaya? Ba jikokina bane" bude bayan motar tayi ta shiga, ya girgixa kai yace "Kina da hankali kuwa Rachael, kan ki daya kuwa? Ina xaki da yaran mutane" fitowa tayi daga motar tace "You're wasting my time David" daga haka ta k'ara ma sayyadarta mai ta dau hanyar gida uwa xata tashi sama, ya dafe kai yace "My God!" Yakumbo na shiga parlon Col ta gansa xaune da laptop, ya mike ganinta yana murmushi yace "Sannu da xuwa yaya" tace "Sannu Ahmad, na same ku lafiya" yace "Lafiya lau, ashe kin taho baki yi waya ba" tace "Kaga ma ni na mance wayar a gida ban da yanxu da kayi magana" xaunawa tayi tace "Ya muka ji da wannan bakar masifar, wai Aliyu ya dawo da yara, anya Ahmad baka yi masa baki ba kuwa" Col ya girgixa kai yana murmushi yace "ko daya" tace "To ita kiristar tana ina?" Col yace "Tana gidan, yanxu uwarta ta xo ta kwashi yaran ma" Yakumbo tace "Wasu yaran kuma?" Col yace "Yaran dai, baki gansu tsatstsaye parlor ba" mikewa Yakumbo tayi tace "Xata ina da su? tare da uwar yaran ta tafi?" Col yace "Xata raine su mana, ba yar ta bace ta haife su, Uwar yaran na nn parlor...." Yakumbo tace "Ban gane xata raine su ba?" Col yyi yar dariya yace "Ae fa tana da gaskiya yaya, jikokinta ne ai" ta rike kugu ta saki baki tana kallonsa, can tace "Ae ni dama tun ba yau ba nasan kai mugu ne Ahmad, wllh kai mugu ne, to muguntar taka ta sojoji sai ya kare a kan mu? ta kwashe min jikoki ka bar ta ta fita? Toh Allah ya fika" Bata jira cewarsa ba ta fice parlorn ta dawo kasa, tana kallonsu Hajiya Mariya da har lkcn suka kasa xaune, Noor kuma sai rusa kuka take, a fusace tace "Amma ku dai anyi gayyar yu yu yu, yanxu duk yawan ku a parlorn nn ku ka bar figaggiyar mata ta fice da 'ya ya har biyu?" Hajiya Mariya tace "A'a Col ne yasa ta fita da su, shi ya hanamu aikata komai wllh" a mugun fusace Yakumbo tace "Yo dama sai ku kula wnn da ya baro hankalinsa gaba daya a yak'in biafra?" Hajiya Mariya ta tabe baki tace "To ina mu ina ja da shi yaya?" Yakumbo tayi wani shewa tace "xata san jikokina ta fita da yau, kin dai san gidan koh?" Hajiya Mariya tace "Na sani" Yakumbo tayi kofa da sauri tace "Mu je" Hajiya Mariya ta dau Hijab din ilham ta bi bayanta, tun da suka dau hanya Yakumbo ke bala'i uwa xata tashi sama, col kam ya sha xagi har da na sayarwa, Hajiya Mariya dai sai bin ta take don tana da assurance baxa su fito gidan ba sai tare da yan biyu, suna isa gidansu Noor yakumbo bata saurari mai gadi dake neman sanin wanda suke nema ba ta bangajesa ta shige gate tana cewa "Kaji min mai gadin gidan bala'i" Hajiya Mariya ta bi bayanta, tsaye suka ga Mr David a balcony abun duniya ya ishesa, Yakumbo ta kalli Hajiya Mariya tace "Ita ce wnn" Hajiya Mariya na kkrin danne dariyarta tace "A'a ba ita bace" Yakumbo bata kuma kallonsa ba ta shige parlorn, bbu kowa ciki, Yakumbo ta haura sama Hajiya Mariya na biye da ita, dakuna suka dinga bubbudewa har suka bude wani wanda da alamar na Rachael ne, kwance suka ga yaran duk biyu a kan gado, Rachael na tsaye a press din kayanta xata fiddo xani da xata goya daya, ta rike daya su tafi church, duk a tunaninta David ne ya shigo shi yasa ko kallon inda kofar yake bata yi, Yakumbo ta karasa a hankali ta kinkimi yaro daya tace "Toh Wllh wllh na sake ganin sheggun kafafuwan ki a gidan K'ani na sai na ari bindigarsa na harbe su" A firgice Rachael ta juyo, Hajiya Mariya ta dau daya yaron da sauri, Rachael tace "Jesus Christ me ya kawo ku gidana?" Yakumbo na nuna ta da yatsa tayi mitsi mitsi da ido tace "Abinda ya kai ki gidanmu daxu" Tuni Hajiya Mariya tayi waje da Sadeeq, Rachael ta bi ta da sauri tana cewa "Ki dawo da yaran nn kar a ji mu a police station, ki dawo ki ajiye min jika na...." Yakumbo ta bi bayanta tana cewa "Aji mu a bariki karewar station, kin yi kadan ki shigo har gida ki kwashe ma mutane yara yar banxa kawai, ke kika yi cikin da aka haifesu xaki kawo mana rainin wayo" ai tuni Hajiya Mariya ta fice parlon gidan, Rachael dake ta vibrate ta juyo tana kallon Yakumbo tace "Amma ai 'ya ta ce ta haifesu ba wani ya haifa mata su ba, i swear to God of Jacob baxa ki fitar da yaron nn gidan nn ba yau sai dai duk abinda xai faru ya faru" Yakumbo tayi shewa tace "Dambe xa mu yi knn, to tsaya" cire mayafin kanta tayi ta goya jaririn da ya fara kuka tsabar wujjigasa da take, ta daure sa tamau a baya snn tace "Toh taho" David ya shigo parlon yana kallonsu, a tsawace Yakumbo ta kuma cewa "Ki taho nace ki karbesa, ban da raini har kya je gidan mutane ki kwaso yara, yo ai yar ki ya kamata ki kwasa ba su ba, su da suke gidan Ubansu" David yace "Kiyi hakuri don Allah" wani kallo ta jefa masa tace "Da xata can baka bata hakuri ba sai ni da na xo daukansu xaka ba hakuri" daga haka tayi hanyar kofa tace "Ashe dai karamar hauka ke kanta, nayi xaton sai mun dambatu xan bar gidan" ko rufe masu kofar bata yi ba ta kara gaba abunta, Rachael ta fashe da kuka tana kallon David yace "Serves you right" daga haka shi ma ya bar mata parlorn, yakumbo ta dinga masifa ita kadai a hanya ga yaro sai tsala kuka yake a bayan ta, ta kai masa duka a baya tace "Kai don mahaifinka rufe min baki kar in ajiye ka a nan inyi wucewata, baka gode Allah naje na amso ku a hannun kafura ba, in dan ta kakan ka ne ai sai dai kayi ta xama a gidan, mata yar banxa kawai ta xo ta kwashe ku, ita Hajarah ta tsaya tana kukan makirci ta kasa kullala komai" Hajiya Mariya na shigowa parlor Hajiya Rahina tace "Alhmdllh, har naji sanyi, amma wnn fitina da me yyi kama" Ummi ta sauke ajiyar xuciya tace "Allah ya kyauta" Mami kam kasa cewa komai tayi, Hajiya Mariya na bude yaron da ta lullube da xani sbda sanyin waje sai da tayi shock ganin Rosary a wuyarsa, bakinta a leko ta cire ta ajiye a kasa, sai ga Yakumbo ta shigo goye da Abbakar dake tsala kuka, sauke sa tayi tace "Da alama yaran nn yafi son can ne, bnda munafurci muna baro gidan ya dingi tsala min ihu har na iso nn, to tsaye xa mu yi a kansa don abun kunya daya ya ishe mu ba sai an mana k'ari ba" salati ta xabga bayan ta saukesa tace "Mayya, har ta rataya masu sarkan coci a wuya" sai kuma ta fashe da kuka tace "Duk Ahmad ne ya ja maku, bbu dole sai Aliyu ya tattara ya bar gidan tunda tun yanxu ya fara nuna masa bai son 'ya yansa, to ni idan ban so 'ya yan Aliyu ba 'ya 'yan wa xan so, dubi fa yaran kyawawa da su kamar larabawa..." Mami ta mike ta bar parlon, Yakumbo ta cire Rosary din ta jefar tace "Allah ya raya min ku a tafarkin islama, yasa ku xama manyan malaman islama irinsu Isma'il Mufti Menk a can waje da kuma fantami a nan Nigeria" murmushi Ummi tayi tace "Ameen" Yakumbo ta nufi sama tana cewa "Kuma Allah ya raba ku da hali irin na Aliyu, kwakwalwarsa kawai nake son ku dauko" parlon Col ta shiga tace "Toh naje na karbo su Ahmad, gari na wayewa kuma xa su bar maka gidan ka tunda ba son su kke ba, kai da ganinsu kuma kila sai dai girmansu" tana magana ne hawaye cike idonta. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 97..... Hajiya Mariya ta kwankwasa kofar dakin Abuturrab dake xaune tare da Noor a dakin yyi lallashin har ya gaji ya xauna yana kallonta shi dai yasan sai in Yakumbo bata je gidan ba amma ko da tsiya sai ta dawo tare da yaran, mikewa yyi ya bude kofar yaga Hajiya Mariya tsaye da Sadeeq hannunta ta mika masa shi tace "Bata yaron ta" d'an murmushi yyi ya karbi yaron bai dai tambayeta d'an uwansa ba ya juya ya koma dakin, ajiye ma Noor yyi a jikinta, ta kallesa tace "Dayan fa?" Yace "Yana gun su" cikin rawar murya tace "Kila baya wajen su" Dago kanta yyi yana kallon kwayar idonta, can ya langwabar da kai yace "Baby shknn yanxu duk son da kike min kin kwashe kin mayar kan twins, to ni meye tawa makomar, naga kamar ta babies kadai kike yi ynxu" dauke kanta tayi bata ce komai ba, aka bubbuga kofar dakin ya mike yace "Toh ga shi nn shima an kawo maki" bude kofar yyi yaga yakumbo ce ta shigo dakin rike da Abubakar ta kwantar da shi tace "Aliyu, toh dai a ynxu Ahmad bai da babban makiya kamar wa ennan 'ya yan naka, idan xaka ji ta nawa ka tattara ina ka ina ka, suma ka tattara masu ina su ina su ku bar masa gidan sa, ranan da Allah yasa suka girma sai su tako da kansu su xo su gaishesa, ni ba ma wnn ba, gani nake kamar bak'in cikin rahamar Allah yake masu, to banda haka ta ya xai bar mata me xuwa coci ta shigo masa har gida ta kwashe su ta tafi dasu, kasan matar har ta rataya masu sarkan coci fa a wuya Aliyu" Noor dai sunkuyar da kanta tayi tana wasa da yatsunta, shi kam Abuturrab bai iya yace komai ba sai kallonta yake, Yakumbo ta tabe baki tace "Toh dai Allah yyi mana tsari kwashi yaran ka ka bar masa gidansa da wuri wuri, yara maa sha Allah haka" kallon Noor tayi tace "Ke kam kinyi sa'ar uwa, toh ke ma har yanxu kina xuwa cocin kenan koh?" Abuturrab yace "A'a ita musulma ce..." Ta d'an yo waje da ido tace "Tohhh ta musulunta knn, amma dai da xa ka ji ta nawa ka samu yar uwarka musulma warce xata sa ta da 'ya yanta a hanya ka aura kwanan nn..." Sai a snn Noor ta dago manyan idonta tana kallonta, Yakumbo tace "Atoh, ni bayin Allah nake ji ma kar wataran ta mayar da su ruwa, ita ma ai tasan irin musuluntar da suke yi, bari in samu Hajarah in ji ynda xa ayi" daga haka ta fice daga dakin tana cewa "Mu muka ga kaddara, mun kuma gode Allah da ya ba mu ikon daukarta a ynda ta xo mana amma dole ya kara aure don daidaituwar gidansa" Abuturrab ya d'an kirkiri murmushi ya kamo hannun Noor ganin mood dinta cikin sanyin murya yace "You are the 1st nd the last in shaa Allah wife, no amount of talks will make me change my mind" ita dai bata ce komai ba sai hawaye da ya sakko idonta, rungumeta yyi ya lumshe ido yace "Believe me mum twins" Yakumbo na fita ta bude dakin su Ramla, Khaleesat da fatima ne a dakin, Khaleesat ta taso ta rungumeta tace "Umma yaushe kika xo" Yakumbo tace "Tun daxu fa, sai na tarar an dauke yaran da na xo gani shine na tafi karbo su, wacece wancan kuma" Fatima ta ajiye wayar hannunta tace "Ina yini" Yakumbo tace "Lfya lau" Khaleesat tace "Bakuwa ce Umma" Yakumbo tace "Ayyo, sannun ki toh" daga haka ta yi gaba, dakin Mami ta shiga, ta kalli su Ummi dake xaxxaune dakin da Hajiya Mariya tace "Toh dai Hajarah mijin ki ya nuna baro baro bai son xaman Aliyu gidan nn tunda har ya fara barin kafura na kwashe yara, don haka nace Aliyu ya lallaba ya bar gidan ko ko ya kika ga?" Hajiya Mariya tace "Gaskiya ne yaya, kuma tun da har taji ddin shigowa gidan gobe ma sai ta iya xuwa tace xata dauke su" Yakumbo tace "Wayyoo Allah Mariya, ke da kika san komai...." Xaunawa Yakumbo tayi tace "Abu na biyu kuma, Hajarah cewa nayi ya kamata Aliyu ya kara aure kwanan nn, ya auri musulma yar uwarsa warce xata sa ma 'ya yansa ido, Allah na tuba tubabbiya bbu wani tarbiyar arxiki da xata iya ba ma yaran nn biyu abun tausayi" tun da ta fara Hajiya Mariya da su Ummi ke kallonta, ta ci gaba "Shine nace in fara shawara da ke kafin in koma gun Ahmad, ko ya kika ga, ita wnn din ba wai ba ma sonta bane, a'a kawai jikokinmu muke ji ma, gwara ya auro cikakkiyar musulma yar uwarsa ta xo su hadu a ba yaran tarbiya, to ni da nake son su xama manyan malamai ma...." Mami tace "Toh, idan hakan ne mafi alkhairi Allah ya tabbatar...." Mikewa Hajiya Mariya tayi a fusace tace "Amma yaya baki kyauta ba in har kika fadi hakan gaskiya" Yakumbo ta yo waje da ido tace "Bata kyauta ba? Shi addu'ar da tayi ne bata kyauta ba Mariya?" juyawa Hajiya Mariya tayi ta fice daga dakin, Yakumbo tace "Ji sha sha sha kamar ba da ita muka je muka yi cacan baki aka bamu yara ba, Mariya fa ba cikakken hankali ke gareta ba, ko don bata san xafin haihuwar bane oho, banda haka yaya ana nema ma yaro abun alkhairi ta hayyako mana haka, so take 'ya yan sa su tashi bbu addini ne ko yaya, ai ni Aliyu ya gama cutar mu" Hajiya Rahina tace "Ae kam maganar ki na kan hanya Hajiya, uwa fa ke ba yara tarbiya ba uba ba...." Ummi ta katse ta tace "Amma ita ma ba jahila bace totally a islam kakanta musulmi ne, haka kuma kanwar mahaifinta, baka taba cewa ba musulma bace ita idan ba kun xauna tare bane" Mami tace "Ae ba don a walakantata ba Yakumbo ta fadi haka" Yakumbo tace "Atoh fada masu dai, kin san idan jika ba naka bane" daga haka ta fice daga dakin tana cewa "K'arin Auren Aliyu ba fashi wllh" Hajiya Mariya da ranta ya gama baci ta sauka kitchen ta ci gaba da taya Anty Maryam gyare gyaren da take da yaran frnds din Mami. Mami tayi murmushi tace "Shknn kinga sai a hada su da fatima Hajiya" Ummi tace "Wace fatiman?" Mami tace "daughter nah mana" Ummi ta girgixa kai tace "Allah ya kiyaye, Aliyu da matarsa sun wuce haka a gu na" Mami tace "Kamar ya Allah ya kiyaye, Hajiya idan kika duba maganan da Yakumbo tayi xa ki ga gaskiya take fadi wllh, ni ba wai bana son matar nn tasa bace kawai dai makomar yaran nake jimami, kinga shi kansa Aliyun ban da yyi sllh kan lkci sai kauce ma sa6o bbu abinda yake na addininsa, Idan ba kwanan nn da naga Aliyu ya fara tsayuwar dare ba shi ba gwanin yin hakan bane, Azkar idan yyi na safe a da can toh bbu xancen na yamma, Karatun qur'aninsa ganin dama ne, to ina gida a nn don Allah, me xata gani a gunsa da har xata yi koyi da shi ita matar? Amma kinga idan ya aure wata daban sai ta sa su kan hanya gaba daya" Ummi ta tabe baki tace "Toh Allah ya basa wata daban din" Mami tayi murmushi tace "Fatima ce ba wata daban ba" Ummi tace "Ita Fatimar ca aka maki rike take da addini banda sllh da take?" Dariya Hajiya Rahina tayi, Ummi tace "Atoh, barin yaran ynxu da bnda kishin hauka da bala'i bbu abinda suka sa gaba, ke a tunaninki xa ki nemo mai addini ki hada su amma karshensa xamar kishiya xata yi da ita ayi ta kishin hauka mara amfani, am nt in support of this gaskya Mum Aliyu, ita kuma sai aka ce a haka xata yi ta xama baxa ta nemi ilimin sabon addinin nata ba, ina ce a nan su Hajiyar Shagari qtrs take gaya mana tayi converting a gun su.... Ayi mata adalci, da rashin yan uwanta xata dinga ji ko kuma da kishiyar da ake shirin laka6a mata, bata da kowa da tafi kusanci da a yanxu ban da mu, kar a canxa mata view dinta a kan islam, in her case yi mata kishiya is totally out of the point, snn kun san duk namiji idan ya kara aure irin rawan kan da yake, Aliyu won't be exceptional, ko da kuwa ya nuna baya so to fa wataran xai so ne, For the sake of her conversion a cire maganan kishiya pls, ko da xai yi ya bari sai sun dade tare idan da rai da lafiya ta cika masa gida da 'ya ya...." Hajiya Amina dake ta jin su ta sauke ajiyar xuciya tace "Haka ne Hajiya you have a point, yakumbo tayi hakuri da wnn xancen, ke Mami ki nuna baki amince ba kawai" Mami bata ce komai, Ummi ta mike ta fita daga dakin, Ko da yakumbo ta kai ma Col xancen karin auren Abuturrab shiru yyi yana saurarenta, can ya gyada kai bayan ta kai aya yace "Kina da point a nan yaya" *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 98..... Washegari da sassafe Ummi ta gama shirinta ta sa fatima ma ta shirya ta dau jaka tana kallon Mami tace "Toh Hajiya xa mu koma garin mu sae mun yi waya, Allah ya raya Ahmad da Abbakar" Mami tayi murmushi tace "Irin wnn sammako haka, ko duk maganar jiya ce" Ummi tace "Haba ko daya, ina son isa da wuri ne don inje clinic" Mami ta mike tace "Toh shknn Hajiya, mun gode kwarai Allah ya kara dankon xumunci" Ummi tace "Ameen" Naman suna me yawa Mami ta tula mata da drinks sai snacks tace ta kai ma su Rabi'a, A parlor Ummi tasa aka kira mata Abuturrab, ya sakko ganinta yace "Mami har xaku wuce da safe haka" tace "Eh ina son mu isa da wuri ne, sai ka turo babban mota a kwashe maku kayan ku na can ko boy" ya d'an shafa kai yace "Toh Mami, bari in kirata ku yi sallama" tace "A'a bar ta kace mata mun tafi kawai," a hankali yace "Toh ina xuwa Mami" daga haka ya tafi daki ya dauko makullin motarsa don ta taho masa da motar tasa daga can gombe, tare da Hajiya Mariya suka tafi kai su park, ya ba Fatima dubu ashirin taki karba, dole Hajiya Mariya ta tilastata ta karba tace ta gode, yana kallon Ummi yace "Nagode Mamina sai mun xo kawo maki xiyara in sha Allah, ki gayar min da kanwata khadija" tace "Toh ina xuba ido boy, ga dai Samha nan amana, idan ka ci amana kuma kai ma kasan sauran Aliyu, Allah raya maka boys dinka a tafarkin islam" cikin sanyin murya yace "Ameen Mami" tace "One more thing Aliyu, you re educated, you knw what's right from wrong... This is all i have to tell you ka xama me aiki da hankalin ka" daga haka ta shiga mota ta ce "Toh Hajiya Mariya sai mun yi waya, Allahu ya bar xumuncin mu" basu tafi ba sai da suka ga motar ya tashi snn suka dau hanyar gida, Abuturrab na driving ya kalli Hajiya Mariya da har lkcn bata da walwala yace "Mum wani abu ya faru ne, ur mood isn't encouraging" sai a snn ta kallesa tace "Tunda wnn fitinannar Uwar taka ta xo meye ma baxai faru ba, mata bata da aiki sai hada fitina, kaga xan kira Alhaji, (wato mijinta knn) in nema maka alfarma ya baka gidansa daya dake hotoro ku koma can da xama a yau Aliyu.... Yayar babanka ba da alkhairi ta xo ba gaskiya, naga kuma kamar Mami na neman biye mata ne" Abuturrab ya d'an yi shiru, sai can yace "Cewa take sai na kara aure koh?" Hajiya Mariya tace "Ta gaya maka kenan?" Gyada kai yyi yace "Eh, ta fadi hakan gaban Samha ma" Hajiya Mariya ta girgixa kai tace "Muna komawa gida ynxu ku fara shiri, dama Col ba son xamanka yake a gidan ba naga alama, ku koma hotoro kawai, but before then xaka bar su a gidana su yi arba'in" yace "Mum to gidana fa?" Tace "Aa bn san col ya san inda kake ma" Bai kuma cewa komai ba har suka isa gida, yana biye da ita a baya suka shiga parlor, xaunawa yyi a parlorn ya gaida Anty Maryam ta amsa, ya jawo Ihsan yace "Anty amma xaki bar mana ihsan koh" dariya kawai tayi tace "Lallai kam, xuwa anjima xa mu wuce" yace "Da wuri haka Anty" tace "Shekaranjiya na xo ai" yace "Toh Allah kai mu Anty" tace "Ameen" ya mike yana murmushi yace "Da gaske fa Anty xa ki bar min ihsaan" murmushi kawai tayi ya nufi stairs, bedroom dinsa ya shiga, ganin Noor bata dakin ya fito ya shiga dakin Maminsa, Yakumbo ya tarar tana ma Abubakar wanka, Mami na xaune rike da Ahmad, Ya xauna gefen gado yace "Ina kwana Umma" tace "Lafiya lau, sai yanxu?" kallon Mami yyi ita ma ya gaida ta, Ta amsa tace "Har sun wuce" Yace "Eh sun wuce" mikewa yyi ya fita daga dakin ya koma nasa, xama yyi yana tunanin maganganun Hajiya Mariya, can ya sauke ajiyar xuciya ya mike ya shiga bathroom don yin wanka, ko da ya fito daga wanka, xaune ya tadda Noor a can karshen gado a shirye cikin riga da skirt, ga breakfast da aka ajiye mata kan rug, ya ajiye karamar towel din hannunsa ya karasa kusa da ita yace "My wife" bata ce komai ba ya kalli abincin dake kasa yace "Toh sauka ki yi breakfast mana dear" nan ma tayi shiru, ya dago kanta yana kallon kwayar idonta yace "Tell me, wani abu ya faru ne" hawaye ya gani cikin idon, cikin Sanyin murya yace "Wife...." Still bata ce komai ba, a hankali yace "Ni bn san meyasa closeness din mu ya ja baya ba Samha, we were nt like this before, it's getting worst now, baki son amsa ni idan na maki magana, you derive pleasure ignoring me always.... I don't just knw what came over you" mikewa yyi ya dau towel dinsa ya koma can daya side din ya xauna, can ya tashi ya fara shiryawa har ya gama bata dago kanta ba, kofa ya nufa ya fita daga dakin, kuka ta fara a hankali, tayi me isarta snn ta sakko kasa, dai dai shigowar Yakumbo, ta kwantar da yaron hannunta tace "Ynxu 'yar nn barin abincin kika yi ya sandare" girgixa kai kawai Noor tayi, tace "Toh maza ki gama ki basu abinci su ma don yunwa suke ji" a hankali tace "Toh" yakumbo ta fita, Hajiya Mariya ce ta shigo da Sadeeq ta kwantar da shi gefen d'an uwansa tana kallon Noor tace "Idan kin gama sai ki yi breastfeeding dinsu kin ji Daughter" Noor tace "Toh" ita ma ta fita dakin, Tea kawai ta hada ta sha don ji tayi baxata iya cin komai ba, can ta mike ta koma kan gadon ta kwanta gefen yaron tana kallonsu. Karfe sha biyu saura Anty Maryam ta wuce, Col da kansa ya bata 20k kudin mota, Mami kuma ta ba Ihsaan atamfa guda Uku cikin wanda twins suka samu na suna, Hajiya Mariya da Abuturrab ne suka kai ta park, tun da suka bar gidan Noor ke kuka a daki, ta rasa dalilin kukan nata. Abuturrab na dawowa Ilham ta tare sa a parlor wai Abba na kiransa, ya d'an yi jim yana kallon Hajiya Mariya dake kallon ilham ita ma, can tace "Yakumbo na parlorn ne?" Ilham tace "Eh tana ciki" tsaki Hajiya Mariya tayi ta wuce sama, Abuturrab ya nufi parlon Abbansa, a hankali ya tura kofar ya shiga da sallama, xaunawa yyi kasa yana kallon Col yace "Ga ni Abba" Col ya kallesa yace "Na gan ka" D'an murmushi yyi ya sunkuyar da kai, Yakumbo tace "Atoh, ba wani abu bane dama batu ne da xai xame maka alkhairi nn gaba, kaga dai ni Fatima baxan so abinda xai cutar da kai ba Ali, kai ba ma hka ba, ni ta wa ennan yara biyu nake baxan so su halaka ba, haka kurum rana tsaka ka dau kirista wacce ba muharramar ka ba ka lula duniya da ita, kayi ta ba Ahmad wahalan neman ka, ni ma kasa nayi ta shiga da fita ina neman a karkato min da hankalinka ka dawo gida, to ni duk wnn bai wani dame ni ba, abinda yafi damuna shi ne Hajarah da Mariya sun san komai suka dinga munafurtar mu ashe su suka xuga ka kayi abinda kayi ma, kuma sun san inda kke, to ba wnn ba ma, babban tashin hankalin shine ynda ka kai yarinya masallaci aka daura maku aure kaje kana rayuwa da ita hankali kwance ga ka tatattcen mara ji koh? to dai wllh kullum kayi ta addu'a Allah ya yafe maka mahaifin ka ya yafe maka ni ma in yafe maka, idan ba haka ba wllh tarihi sai ya maimaita kansa, kana ji kana gani yar ka mace xata bi kato su gudu da sunan so, to don Allah wa ka cuta idan ba mu ba?" Sai a snn Abuturrab ya dago yana kallonta, Tace "Atoh, ba xancen ka harareni bane gaskiya ce na fada, ba haka kayi ma yar mutane ba, to kaji tsoron Allah kar kai ma ayi ma yar ka, kaga ko mu ma mun shiga uku ba kai kadai ba, to ni duk ba ma wnn ba, wai sai gashi da ka tashi dawowa sai ka dawo mana da yan biyu, wai kirista ta haife su, to ynxu abun tambaya a nn Aliyu shine, waye xae ba yaran nn tarbiya irin ta koyarwar islama?" Bbu yabo bbu fallasa yace "Uwarsu!" Yakumbo tace "Yau naga abinda ya ishe ni bai ishi Allah ba, wace uwar ta su? Ita kafurar xata ba su tarbiya" Abuturrab yace "Umma ki bar ce mata kafura, ynda kike musulma ita ma haka take musulma, kuma bbu wanda yafi wani a gun Allah sai...." Tsawa Abba ya daka masa ya mike yace "Are you stupid, ko ka fara shaye shaye ne?" Yakumbo tace "Atoh wa ya sani abu a duhu" Abba yace "I will kick you out idan baka maida hankali kasan warce ke gabanka ba, kar kayi tunanin na basar da abinda ka min ne, i am coming for you soon" Yakumbo ta tabe baki tace "A'a bar sa, ba ga yaran maxa nn ya haifa har biyu ba, xai ji ko da ddi ko bbu" Abuturrab bai kuma cewa komai ba, Tace "Toh ae ba tsoron ka ake ba, kame kamen ma an fasa, dama ba wani abu bane yasa aka kira ka nn, aure nake son kwanan nn ka sake, ka auri wacce xata kula maka da yaran da ka haifa, ta kuma yi musu tarbiya irin ta musulunci" tana huci ta kare maganan, ya d'an kalleta, snn ya girgixa kai yace "Bani da ra'ayin auren mata biyu Umma kiyi hakuri" ta mike tace "Toh kuwa ynxun nn xaka yi ra'ayin yin haka, idan ba haka ba wllh wllh wllh in kwashe yaran inyi tafiyata da su su girma a gu na, bbu kai bbu su kuma" Abuturrab yace "Na baki Umma" buda baki tayi tace "Ohh haka ma kace" yace "Umma ni dai da in kara aure gwara kin tafi da su ki basu tarbiyar ke, ita kuma nayi alkawarin baxa ta sake haihuwa ba.... Ina ce sbda a ba yaran tarbiya xan kara auren" rike baki tayi tace "Ehh lallai Aliyu ya xama dan iska, toh kai ke bada haihuwan da xaka hanata yin sa?" Ya girgixa kai yace "Bani ke badawa ba, amma bayan yaran nn biyu baxa ta kara haihuwan ba bare a dinga tunanin irin tarbiyar da xa su samu, wa ennan da ta haifa dai na baki su ki basu tarbiyar" Col dai kallonsa kawai yake, Yakumbo aka rasa abun cewa sai huci take, komawa tayi ta xauna tace "Toh wai ma ni me xanyi da jikoki daga gun tubabbiya" ya girgixa kai yace "Yara na ne ba nata ba, ni ke da iko da su ba ita ba, snn kuma nace na baki su Umma" a fusace Yakumbo tace "Toh ni kuma jikoki biyu sun min kadan don ubanka" murmushi yyi yace "A'a fa Umma jikokin ki sun kusa sha biyar, to me xai dame ki," Col yace "Alryt, idan kuma ku ka sake haihuwa i will surprise you Aliyu, xaka sha mamaki wllh, lastly ina son ku bar min gidana yau, enough is enough, tashi ka fita" mikewa yyi yace "Nagode Abba" daga haka ya juya ya fita parlon, ko da ya shiga bedroom din Mami, samun Hajiya Mariya yyi tana ta hada kayan babies, ya xauna gefen gado ta dawo kusa da shi tace "Me suka ce" d'an murmushi yyi ya gaya mata ynda suka yi da Yakumbo da Abba ta tabe baki tace "Toh kar ka kuskura ka cuce yar mutane, koma meye gwara kayi a kanka" Dariya yyi yace "Ni in cuce kai na kenan Mum?" Tace "Atoh ni ina ruwana, am very serious don't make her use anything but you can" yace "Uhmn to shkkn Mum" ta mike tana ci gaba da abinda take tace "Gwara da kace masu haka ai, ita kuma sai in ga nonon da xata ba yaran" dariya yyi ya nufi kofa tace "Ku shirya ynxu Aliyu" yace "Toh mum" daga haka ya fita. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 99___100 Bedroom dinsa ya shiga ya tadda Noor kwance, yyi mata kallo daya ya dauke kai ya nufi gun kayansa, cikin kankanin lkci ya gama hada abinda xai hada ba tare da ya kalleta ba ya nufi kofa ya fita, dakin mami ya shiga Hajiya Mariya tace "Har kun gama?" Yace "Ehh" ya kalli Mami dake kallonsa ya xauna gefenta yace "Ki yi hakuri Mami, everything will come to past by the grace of God, i knw i have made u pass through so many pains, ki yafe min Mami don Allah" bata iya tace "Komai" Hajiya Mariya tace "Allah ma albarka" a hankali yace "Ameen" har lkcn idonsa na kan Mami, cikin sanyin murya tace "It's nothing Abuu, watarana sae lbri" rungumeta yyi ya lumshe ido yace "Nagode Mami" ko da suka fito dakin Hajiya Mariya na janye da babban trolleyn da ta tula kayan yara da na Noor tace "Ce mata ta fito son, u help her with the boys" yace "Mum i dnt knw hw she will feel idan ta ji xa a raba su da yaran da ki shiga ki mata mgna" Hajiya Mariya ta tabe baki tace "Duk fa baraxana ce, ya xata yi da 'ya yan mutane har biyu" murmushi yyi yace "Toh mu ma sai mu yi baraxanan bata su mu ga ko xata karba" Hajiya Mariya ta sake trolleyn ta shiga dakin, ganin Noor kwance tace "Baki shirya ba Daughter?" Mikewa xaune tayi tana kallonta, Hajiya Mariya ta dau Ahmad ta fita da shi ta mika ma Abuturrab snn ta dawo ta dau dayan tace "Kafin in dawo ki hada abinda xa ki hada kin ji, xa mu je can gida na ne" sosai Noor taji ddin hakan a ranta don ji tayi bata son xaman gidan kwata kwata, Abuturrab na rike da duk yaran ya shiga parlon Abbansa da sallama, gun Yakumbo ya nufa ya mika mata su yace "Ga su Umma, xa mu tafi ne." Ta yo waje da ido tace "Ina?" Yace "Duk inda Allah yyi!" Tace "Guduwan xaka sake yi knn" ya girgixa kai yace "Abba ne yace mu tafi" tabe baki tayi tace "Munafuki dama can kana da niyyar yin hakan ne, bnda hka ta yaya daga magana xaka kwaso min 'ya ya kace xaku tafi, anya kana son rabuwa da mu lfya kuwa Aliyu?" Yace "Ba haka bne Umma, bna son bacin ran Abba shi yasa xa mu tafi ynxu" tace "Ka ji salu6abbe, yo bacin rai na nawa, duk wa enda ka sa shi a baya ce maka aka yi ya warke a xuciyarsa ne, to ni ba wnn ba, ynxu da ka kwaso min yara ya xan yi da su?" Yace "Umarnin ki fa na bi Umma" kallon Abba da bai ko kalli inda suke ba tayi tace "Ahmad kana jin gantalallen d'anka koh? Ka tambayar min shi ya xan yi da su, nono garen da xan basu ko yaya" Abba yace "Ki barsa ya tafi da su kawai Yaya, lkcn da xai yi auren ma ba shawara yyi da mu ba bare har a damu da 'ya yansa, sai dai idan suka xama abinda kike gujen masa bbu shegen da xai ce jikokin Col Ahmad ne" Yakumbo tace "Atoh, su je kawai, amma fa da sun shekara xan bi sa duk inda suke in kwaso su" Col bai kuma cewa komai ba, a hankali Abuturrab yace "Am... am sorry dad, forgive me plss" kofa Col ya nuna masa alamar ya fita, ya juya ba musu ya fita dakin a sanyaye. Dariya Hajiya Mariya tayi ganin ya dawo da yaran tace "Sun hakura knn" Mami ta raka su har mota, tana tsaye har sai da suka bar gidan, Abuturrab ke driving din, Hajiya Mariya da Noor na rike da yaran a baya, har suka isa gidan Hajiya Mariya bbu wanda yace komai cikinsu, yyi horn mai gadi ya bude gate ya shiga yyi parking snn ya bude motar ya fito ya bude side din Hajiya Mariya ta fito Noor ma ta fito, yaron hannun Smll mum din tasa xae karba tace "A'a karbi na hannunta" bai ce komai ba, bai kuma kalli Noor ba ya koma bayan booth ya bude ya ciro kayansu ta bi sa da kallon gefen ido, ganin Hajiya Mariya tayi hanyar shiga gidan ta bi bayanta, a parlor ta xauna tana kallon Ahmad dake hannunta, Hajiya Mariya kuma ta wuce daki, a hankali Noor ta dago kanta suka hada ido da shi don yana xaune parlorn shi ma, shi ya dauke kansa, can ya mike ya bi bayan mum dinsa, ba a dau lkci ba Hajiya Mariya ta fito ta karbi yaron hannun Noor tace "Taso mu shiga ciki" Noor ta mike ta bi ta suka shiga bedroom dinta, Kan gado Hajiya Mariya ta nuna mata tace "You feel at home kin ji daughter, ina xuwa in daura girki Hauwa bata iso ba" daga haka ta fita dakin, Abuturrab ya mike ya fita shi ma, kitchen ya bi small mum dinsa yace "Mum xan wuce can gidan ina son in huta ne" tace "Wani gidan?" Yace "Mine" tace "Kafi son can kenan" d'an murmushi yyi yace "Mum it's nothing ae" tace "Toh shknn, amma me yasa baxa ka huta nn ba sai anjima ka wuce" yace "A'a ynxu nake son wucewa" tace "Toh abinci fa?" Yace "am full mum, sai dai gobe idan na xo" tace "Kun yi sallama da ita?" Yace "Ehh mun yi" tace "Toh Allah ya tsare, kayi addu'a kafin ka fita" yace "In sha Allah mum" daga haka ya juya ya bar kitchen din yyi wucewarsa. Washegari misalin goma na safe Abuturrab ya xo gidan Hajiya Mariya, suna daki gaba daya, tana yi ma Noor kitso don ko da suna bata yrda an mata kitson ba ynxun ma lallaba ta tayi ta yrda take mata sai yatsine fuska take, Hauwa mai aikin Hajiya Mariya kuma tana rike da Ahmad tana basa ruwa a feeder d'an uwansa kuma na kwance, Hajiya Mariya ta amsa gaisuwar Abuturrab tace "Sai yanxu Son" yace "Muna tare da Mujaheed ya dawo jiya" kallon Hauwa dake gaishesa yyi ya amsa gaisuwar snn ya dau Abubakar dake kwance yace "Frnd, good morning" Hajiya Mariya tace "Lallai kam frnd, frnd me hana mutane bacci da daddare, kaga Sadeeq din nn fitinanne ne na karshe" yyi dariya yace "Abokin nawa, to Abbana fa" ta kalli Ahmad tace "Shi kuma d'an taya bera 6ari ne, da yaji ya fara shi ma sai ya cafke" kallon Noor da ta sake ma kai tuntuni tayi tace "Ba ku gaisa ba Samha" Noor ta d'an kallesa tace "Ina kwana" a takaice yace "Lafiya lau mum twins" mikewa yyi yace "Na gaishe ku mum, xan je gidan boss dina ne ynxu" tace "Wai Dr Mustapha" yace "Ehh" tace "Har ya gaji da tambayar ka ya bari, xaka ci gaba da aiki a clinic din nasa knn" yace "Sae idan akwai vacancy mum" tace "Ae ko bbu na tabbata xai bari ka ci gaba, yana sonka mutumin" d'an murmushi Abuturrab yyi, yyi mata sallama ya fita. Haka Noor ta ci gaba da rayuwa da yaranta gidan Hajiya Mariya dake basu kulawa yanda ya kamata, ba ita kadai ba har mai gidanta na mugun son Arshaq da Ashraf sunan da Hajiya Mariya take kiransu da shi daga baya, yaran suka yi girma tun kan arbai'n din, sai rigima da tayi masu yawa, gasu kamar larabawa don kyau hakan yasa duk wanda ya gansu sae ya shiga ransa, ynxu kam mai aikin Hajiya Mariya bata da aiki sae na rainon yaran tsabar yanda take sonsu, ko da yaushe suna wajenta, duk da irin nutsuwar da Noor ta samu a gidan don tayi kyau ta kara haske amma bata da kwanciyar hankali don har lkcn gaisuwa kadai ke hadata da Aliyu, kuma sau daya yake xuwa wataran ma baxae xo ba don ya fara aiki a gun aikinsa na da, ita kanta small mum dinsa na lura da take takensa sai dai bata ce masa komai ba tukun, da ya xo duk awannin da xae yi a gidan yana tare da yaransa ne, Noor kam tsakaninsu gaisuwa, abun ya fara damun Noor ssai, sae dai bata iya nunawa, ranan Hajiya Mariya ta kirasa daki ta tambayesa ma'anar behavior dinsa, yyi murmushi yana shafa kai yace "Mum haka take min ita ma" Tace "Kamar ya?" Yace "Ko da yaushe share ni take ta mayar da shi habit dinta ynxu" Hajiya Mariya tace "Haba Aliyu sae kace baka fi ta hankali ba, ynxu sai ka biye mata kamar wani mara tunani" yace "No mum, am just giving her space ne, naga kamar haushi na take ji" tace "Kasan me yasa take maka haka" kallonta yyi bai ce komai ba, tace "Gani xata yi kai ga ka tare da yan uwanka ko wanne na ji da kai, to ita fa, bata da kowa nata kusa da ita ga irin uwar da Allah ya hada ta da, she will always feel dejected idan ta tuna haka" bai ce komai ba, tace "To gaskiya bna son wnn shashancin gashi naga hakan na damunta sosai, ka dinga mata adalci Aliyu" yace "To nima ta dinga min, har ynxu idan abu bai min dai dai ba sai naji xuciyata na min xafi sosai mum, nima ba a son raina nake mata haka ba, but i have no option taki kwantar da hankalinta kuma ba komai ke damunta ba illa kishi ita bata ki kar in sake ma ko wace mace magana ba in dawo muyi ta xama bana xuwa ko ina" dariya Hajiya Mariya tayi tace "How will dat be possible kuma" Sau biyu Mami na xuwa gidan da su ilham ganin Arshaq da Ashraf, ana gobe Noor xa su yi arba'in Abuturrab na gidan tun yamma har bayan isha sbda ruwan da ake, Hajiya Mariya tace "You spend the nyt here sbda ruwa Aliyu" yace "Yea am thinking of that" Noor na daki kwance wajen karfe goma da rabi, har tayi shirin bacci Hajiya Mariya ta shigo mata da yara ta kwantar kusa da ita tace "Baxa ki sha furan ba kuma Samha" tace "Na koshi Mum" Hajiya Mariya tace "Toh shknn sai da safe" daga haka ta fita, Noor ta d'an yi mamaki don in har mai gidanta bai gidan ta kan kwana da su, Hauwa kuma ta wuce gida, ranan da yake nn kuma Hauwa ce ke tsayawa ta kwana da su, bude kofar dakin aka yi ta dago kai, tayi mamakin ganinsa don bata san yana nn ba har lkcn, ya rufe kofar ya karaso cikin dakin har xai kunna Ac ya tuna da yaran dake kwance ya rage kayan jikinsa kawai ya kashe wutan dakin ya nufi kan gadon ya kwanta, turo baki tayi ta mike xaune ta dau Arshaq ta sa shi a tsakiyarsu, ta dauko Ashraf shima ta ajiyesa duk yana kallonta ta koma can karshen gado ta juya masu baya, daukan yaran yyi gaba daya ya ajiye su can gefensa ya dawo kusa da ita, ta mike xaune tana kallonsa, tashi xaune yyi shi ma xata sauka kan gadon ya fixgota, fadawa jikinsa tayi ta fashe da kuka yace "Na rashin gaskiya koh?" A hankali take kukan bata ce komai ba, can yaji a hankali tace "Am sorry...." ya dago kanta yace "For?" Kin cewa komai tayi ta mayar da kanta kirjinsa, ya lumshe ido yana murmushi yace "Sorry for ur new habit baby, in dai kika kashe ni shknn sai kiyi ta rainan yaran ki ke kadai" kuka ta fara yi sosai, ya kai bakinsa kunnenta yace "Alryt baxan mutu ba sai kin haifa min yara shidda koh?" Abbansa ne ya fado masa ya lumshe ido, ita kam gyada masa kai tayi yace "Alryt, tel me u love me" murya can kasa tace "It's nt worth sayin....." bata rufe baki ba ya fara kissing din ta, Nan ita ma ta nuna masa tayi kewarsa fiye da yanda yyi, washegari da sassafe Abuturrab ya bar gidan tun kan Small mum dinsa ta fito, ita kanta Noor bata san ya wuce ba don tunda tayi sllh ta koma bacci, karfe sha daya Hajiya Mariya ta kirasa da yake ranan lahadi ce sai ga shi ya taho, a daki ya sameta bayan sun gaisa tace "Kaga yau suka yi 40 days son, ya kamata ku koma can gidan tare, before then kuma lefen da baka yi mata ba sai kayi xa su koma" dariya yyi yace "Kai mum" tace "Yes in raka ka kasuwan, kuma miye na wucewa da asuba" ya d'an shafa kai yace "Ba komai mum" mikewa tayi tace "Toh ni dai bari in shirya mu je kasuwan ynxu" fita yyi ya shiga dakin da Noor take ya sameta xaune tana ta wasa da yaranta, xaunawa yyi kusa da ita yace "Tom kin gama da su, it's now my time" hararansa tayi tace "Ni bn gama da su ba" rungumota yyi yace "Ashe kema kin yi missing dina baby?" Ta rufe ido bata ce komai ba tana murmushi tana shakan kamshinsa me ddi, murya can kasa yace "yesterday was great...." Bude kofar dakin Hajiya Mariya tayi, Noor ta janye jikinta da sauri, yi tayi kmr bata gansu ba tace "Ina jiranka ne Aliyu" ya mike da sauri yace "Okay mum" tana fita yayi kissing dinta a lips yace "Sai mun dawo baby" bin sa tayi da ido don ba karamin kyau kananun kayan jikinsa suka yi masa ba, yana fita Hauwa ta shigo dakin. Abuturrab ya langwabar da kansa bayan sun isa Atm yace "Mum kudin account dina is nt up to 500k fa, kuma...." Tace "Baka da damuwa sai in ranta maka idan ka samu ka mayar min da kayana" dariya yyi yace "Kai mum" tace "Ehh, xan dai bada tawa gudunmawar kayan jewelries" yace "Toh nagode mum" dubu dari biyu da hamsin kawai ya ciro a account dinsa, ita ma ta cire kudi me yawa bata dai gaya masa ko nawa bne suka shiga kasuwa, akwatuna masu kyau na xamani ta fara sa suka siya set guda, daga nn kuma suka shiga shagunan atamfofi ta siya manyan atamfa guda sha biyar snn ta siya masu d'an saukin kudi guda goma, ta siya lace masu tsada biyar, sai materials da abaya kala kala, mayafai, hijab, jakunkuna, takalma, kayan shafe shafe, turare, sabulai, kai duk abinda tasan ana xubawa a lefe har da su pray mat, alqur'an da carbi, sae jewelries da ta bata lkci wajen xabansu, Abuturrab dake xaune sai kallon ikon Allah yake yace "Mum kashe ni kike son yi kawai" kallonsa tayi tace "Wato ga yarinya ka samu a bnxa koh" dariya yyi yace "Wayyo mum a dai tausaya min, ni fa ne naki" tace "A'a mamar ka na can inda ka baro ta, wnn ce tawa a ynxu" ba su suka bar kasuwan ba sai kusan la'asar, sae da ta tabbatar bbu abinda ya rage bata siya ma Noor ba uwa ynxu xa ayi auren, sai da suka isa gida ta juya tana kallonsa tace "Kudin da xaka ban nayi lissafi 450k bnda kudin jewelries" xaro ido yyi yana kallonta, bata kuma kallon inda yake ba ta fita motar, ta kira mai gadi ya taimaka mata shiga da kaya ciki, Abuturrab ya fito motar yana murmushi a xuciyarsa yace "Lallai mum" Noor bata iya tace ma Hajiya Mariya dake ta nuna mata kayan tana jera su a akwati komai ba, duk jikinta yyi sanyi wanda hakan yasa bata san lkcn da hawaye ya shiga sakko mata ba, jin shirunta yyi yawa Hajiya Mariya ta dago tana kallonta, ganin kuka take tace "Ikon Allah, kuka kuma Samha" dawowa tayi kusa da ita tace "Kukan me kike daughter" rungumeta Noor tayi cikin muryar kuka tace "I love you mum, nagode Allah kara maki tsawon kwana" Hajiya Mariya tayi murmushi tace "Toh Amin my daughter, you take me as ur mother kin ji" karfe biyar da wani abu Hajiya Mariya tayi mata duk abinda tasan ya dace dai na gyaran jiki, ta kira mijinta ta rokesa alfarmar siya masu foodstuffs, ba a dau lkci ba driver ya shigo da buhun shinkafa biyu, carton din taliya uku, jarkan man gyada da manja manya, maggi, gishiri har da kwalayen indomie biyu, Abuturrab na shigowa tace "Toh ga gara nn Alhaji yyi mata nasan har ku bar duniya baxa ka mata gorin hakan ba wataran tunda ku din ba tabbas ne da ku ba, kayan daki kuma in shaa Allah idan kudi ya shigo min xan siya mata nata" dariya yyi sosai yace "Mum you are making me feel ashame, haba my mum" bata sauraresa ba ta kara gaba abunta, bayan magrib Hajiya Mariya ta rakasu can gidan nasu da aka yi furnishing tuni, duplex ne mai kyau da parlor sama da kasa sai dakuna huda ko wanne da bathroom, sannan babban kitchen, xa a iya cewa col ne ya gina masa gidan don kudinsa ba mai yawa bane a ginin gidan, Da yake abban nasa yasan halinsa shi yasa bai yrda ya tare gidan ba da dadewa sai masu gadi har uku dake rayuwa cikin gidan, Kuka Noor ta dinga yi da Hajiya Mariya xata wuce, Hajiya Mariya dake dariya tace "Ae sai yaran ki su maki dariya Samha, kar ki damu ko xuwa jibi Hauwa xata dawo ta dinga xama da ku sai in nemi wata mai aikin" tun barin Hajiya Mariya gidan Noor taki daina kukan da take, ita har xuciyarta take son matar, duk iya rarrashin da Abuturrab yyi mata kin saurarensa tayi, ya kyaleta ya maida hankalinsa kan boys dinsa dake kwance kan gado, ana kiran isha ya tafi masallaci da xai dawo ya dawo masu da take away da fresh milk, shi kadai ya ci don ko kallon abincin ita bata yi, yyi wankansa ya sauya xuwa pyjamas ya kashe wutan daki yyi kwanciyarsa kusa da yaran dake bacci, ta gaji don kanta bayan kusan awa daya ta mike ta shiga bathroom ta dauro alwala ta fito tayi sllh, tana idarwa ta canxa kayan jikinta xuwa rigar bacci don tayi wanka a can gidan, ta je can karshen gado tayi kwanciyarta ta juya masu baya, dawowa yyi kusa da ita ya jawo ta jikinsa murya can kasa yace "Oya ci gaba da kukan" turo baki tayi xata kwace kanta yace "Baki isa ba, ci gaba ina son rarrashin ki yanda ya kamata ne" cikin muryar shagwaba tace "Ni ka bar ni, bana soo..." Tsit tayi ta lumshe ido don bbu bata lkci ya fara rarrashin nata yanda ya kamata kuwa. *Haske writers asso* tnx for d prayers everyone. 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 101..... Zama irin ta masoya Abuturrab da Noor suka shiga yi, bai taba tunanin Noor xata ajiye komai ta fito masa da tsantsan so ba, ko kadan bata son bacin ransa kamar yanda shi ma bai son nata, bbu abinda ya sa ta kara samun kwanciyar hankali irin yanda Abbanta kan xo gidan nasu duk end of month ganin Arshaq da Ashraf da yanxu ke dosan shekara daya, yaran maa sha Allah bbu abinda suka mance na babansu, ga su da farin jini duk inda xa su sai an tanka su, ba don Hauwa dake gidan ba da ba xata iya rainon nasu ita kadai ba don matsalarsu na rigima yyi yawa, Mami kan xo lkci lkci ita ma ganin jikokin nata, wani lkcn kannin Abuturrab kan biyo ta har su kwana gidan amma fa sai ran da Col bai gari, Hajiya Mariya kam dama yaran har sun saba da ita ba a daukan lkci bata je gidan ba, su ma duk sati biyu ko uku su kan je su wuni a gidanta ran lahadi, duk ran Friday Abuturrab kan tura ma Mahaifinsa text din gaisuwa da barka da juma'ah bai taba fashin yin hakan ba, duk da shi ma bai taba masa reply ba, Anty Maryam ma taje gidan nasu sau daya amma bata kwana ba ta wuce, Abuturrab kan je gombe once in a while don gaida Ummi, Noor dai bata taba binsa ba sai dai su gaisa ta waya, Xumunci sosai suke yi da Umma don so tari ta kan je gaida su ta yini da su Arshaq, idan ma suka dade basu je ba, Ahmad kan je ganin takwararsa da matarsa Maryam dake kara koya ma Noor xamantakewar aure, har lkcn idan Noor ta tuna mahaifiyarta fushi take da ita hakan na hana mata walwala kusan kullum kuma sai tayi tunaninta, duk tsawon lkcn nn bata xauna haka ba sau daya Abuturrab yyi mata maganan islamiyya washegari kuma tasa ya kai ta, duk karfe goma take tafiya ta dawo karfe biyu, ita kuma Hauwa tayi rainon yara, ana haka har yaran suka cika shekara daya da watanni biyar nn kuma Hajiya Mariya ta xo ta daukesu tare da Hauwa don ita xata yaye su, duk sai Noor taji ba ddi, wanda hakan sai da ya sa mata xaxxabi, ganin ta ki dawowa normal har bayan sati biyu har abinci ma ta fara ignoring Abuturrab ya sa ta gaba don jin ko an taba ce mata xa a rabata da yaran ne, kasa ce mata komai yyi yana kallon kwayar idonta, lkci daya maganan Abbansa ya fado masa wanda hakan sai da yasa gabansa ya fadi, d'an murmushi ya kirkira yace "Ae shknn sai in je in samu mum in ce mata kince a karbo maki yaran ki" xaro ido tayi tace "Ni ai bn ce maka haka ba" yace "Toh me ke damun ki?" Ta bude masa hannu alamar bata sani ba, hancinta ya ja yace "Fadi gaskiya boys din ki kike tunani" bata ce masa komai ba ta koma tayi kwanciyarta, ya mike yace "On Saturday xa ta kawo su ae wife, ita ma xata je Malaysia ne" fita yyi dakin ya koma parlor ya xauna yyi shiru, can ya mike ya dau makullin mota ya koma dakinta yace mata yana xuwa snn ya fita, pharmacy ya nufa direct, ya siya injections da xai siya da drugs ya dawo gida, bacci ya sameta tana yi, ya kalli agogo ya xauna kusa da ita ya shiga tashinta, a hankali ta bude ido yace "Baki ci abinci ba har ynxu baby" ta girgixa kai tace "Am nt hungry" yace "No u re, tun safe tea kawai kika sha dear, gaya min me kike son ci?" Ta d'an yi shiru sai kuma tace "Tuwo xan ci" yace "Toh bari in siyo maki a eatry" daga haka ya mike ya fita, tuwo da miyar vegetable ya siyo mata yana xuba mata a plate ta sakko kasa, a hankali ta kauda kai, yace "What?" Da kyar tace "I think i want to throw up, ka rufe abincin, it's..." Rufe fuskar tayi gaba daya, ba musu ya dauke abincin ya rufe ya ajiye gefe yace "Toh me xa ki ci" ta mike xata koma kan gado tace "I told you am nt hungry" yace "Noo kin ga akwai xaxxabi jikin ki ki ci ko kadan ne sai in baki magani" tace "Baxan iya ci ba" yace "In kawo maki shayi?" Gyada masa kai tayi ya fita ya hado mata shayin, kadan ya lallabata ta sha snn ya dauko maganin da har ya ballar mata da cup din ruwa ya mika mata ta amsa ta sha, yace "Saura allura" da sauri tace "Bana so" yace "Guda daya fa dear" da kyar ta amince yyi mata alluran snn ta kwanta ya kwashi take away din tuwo da cups ya fita xuwa kitchen, yana fita bacci ya dauketa, a gida yyi la'asar don bai son barin ta ita kadai, karfe biyar saura ya rufe laptop din gabansa ya mike ya wuce dakinta, ganin bai ganta kwance ba ya kalli kofar bathroom dake a bude, ya karasa ciki da sauri, durkushe ya ganta a bathroom din cikin jini, ya dagota yace "Subhanallah what happened, me ya faru, kin ji ciwo ne" a rude yake tambayar ganin kallon da take masa sai da ya sha jinin jikinsa ya kasa cewa komai kuma, a hankali ta mike tsaye ta cire kayan jikinta, Yana tsaye ya kasa cewa komai har ta gama kintsa kanta ta fice bayin, sai a snn ya juya shima ya fita kwance ya ganta kan gado ya karasa a hankali yace "Sannu wife, u were bleeding....." Lumshe ido tayi bata ce komai, pain reliever ya dauko mata yace "Tashi ki karbi magani ki sha pls" bude ido tayi ya duka kusa da ita yace "Pls wife" mikewa xaune tayi ta karbi maganin ta sha, yace "Ina ke maki ciwo" kasan cikinta ta nuna masa yace "Allah xai sauwake kin ji" komawa tayi ta kwanta ya mike ya fita, duk jikinsa yyi sanyi, but he have no other alternative. Kafin kwana biyu Noor ta warware kamar ba ita ba, a ranan Asabar Hajiya Mariya ta dawo mata da boys dinta, har ranta tayi murnan ganinsu amma bata nuna ba, Sai da Hajiya Mariya xata tafi ta tambayeta Anty Hawwa fa, Hajiya Mariya tace "Taje garin su amma sati biyu xata yi ta dawo" Noor tace "Allah ya dawo da ita lafiya" Abuturrab ne ya maida small mum din tasa gida. Haka nn rayuwarsu ya ci gaba da kasancewa gwanin sha'awa, he was very careful kar Noor ta kara conceiving, Har Ashraf da Arshaq suka cika shekara biyu da rabi, a nan ya sa su a islamic schl mai hade da boko, sai a snn Noor tasan ashe Abuturrab ba baya ba a fannin addini kawai ya fi fito da boko fili ne, during weekend gaba daya lkcnsa na gun yaransa yana coaching din su don bai son su yi lacking komai na bangaren addini ynda baxai ji fargaban duk inda xa su shiga ba ko ba ynxu ba, don yasan baxai taba rabasu da dangin mahaifiyarsu ba, mugun tsoronsa yaran suke sbda strictness dinsa ita kuma a lkcn tana shirin fara Diploma a fannin Islamic studies, idan Noor na rera maka karatun qur'an ko tana karanto ma litattafen addini baka taba cewa she was once a Christian, hakan yasa Abuturrab ke alfahari da ita, a cikin kankanin lkci Arshaq da Ashraf suka fara larabci a shekararsu ta biyu a makarantar ga hadda dake kansu, Abbansu ya daina masu Hausa gaba daya sai dai Noor, in dai xai yi communicate da su sai dai Larabci ko Turanci, Mahaifin Noor ya maida gidansu wajen frequent xuwansa sbda jikokin nasa dake mugun sonsa shi ma kuma yake ji da su, ba don kowa yake xuwa gidan ba sai don su, yau ma kamar ko wace Friday Mr David ya xo gidan da yamma rike da chocolates dinsu, yan biyun na xaune gun da Abbansu ya tanadar masu don studies ko wannensu da qur'an a hannu, Noor kuma na kitchen tana girki, duk suka taso gaida kakan nasu, ya zauna kujera yana kallonsu ganin mood dinsu yace "What happen to my boys" Ashraf dai yyi shiru, Arshaq da har idonsa ya kawo ruwa yace "Abbu promise to cane us today" Noor ta fito kitchen ta gaida Abban nata tana murmushi, ya amsa ya maida hankalinsa kan yaran yace "Wht have you 2 done wrong" Ashraf ya juya yana kallon Ummun sa, Mr David ya kalleta yace "Me suka yi" yar dariya tayi tace "Abba k'arin hadda yyi masu tun jiya dan yana nyt duty sai suka ki yi, to yace idan ya dawo daga masallaci xasu bada haddan shine fa ka gansu haka" yace "Toh ke me yasa baxa ki masu ba" tace "Abba basa ji, kallonsu ya fara yawa kwanan nn" da turanci Arshaq yace "Grandpa ai kai ma ka iya ka yi mana" daga haka ya tafi ya dauko qur'an din yana mika masa, shiru Mr David yyi yana kallonsu bai kuma karbi Al-qur'an din ba, Ashraf yace "Pls grandpa, assist us" a hankali Noor ta juya ta koma kitchen, yaran biyu suka kuma hada baki gun cewa "Plss grandpa..." *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 102..... Mr David ya girgixa kai yace "Noo, let me call ur mum to assit you" a tare suka ce "Noo, we want ur assistance Grandpa" shiru yyi yana kallonsu, ganin ynda suka marairaice su ma suna kallonsa, yyi murmushi murya can kasa yace "Alryt, which surah is that?" a tare suka ce "Surah Al-Munafiqun" Lumshe ido yyi yace "Alryt, alryt... you read frm d beginning den i continue frm where u stop" xaunawa suka yi a tare suka ajiye qur'an din hannunsu suka fara karanto haddar suran dake kansu idonsa a kansu ko kiftawa bai son yi.....A aya ta biyar suka dago suna kallonsa, ya dage masu gira yana murmushi yace "Go on boys" Arshaq ya kalli Ashraf yace "We stopped der, ryt?" Ashraf yace "Na'am...." Kallon kakan nasu suka yi, Ashraf yace "Grandpa the next aya is where we need ur assistant" Mr David ya jinjina kai yace "Ohk, ohk go get me pray mat....." mikewa Arshaq yyi ya dauko masa darduma ya kawo masa ya karba ya shimfida snn yace su daura qur'an din a kai, ba musu suka daura, ya sakko kasa ya xauna kan lallausan carpet din parlon ya tankwashe kafa yana kallon qur'an din dake kan darduman, Noor dai na tsaye kitchen ta jingina da bango duk jikinta yyi sanyi, lkci daya hawaye ya kawo idonta, a hankali Mr David ya soma karanto masu aya ta shidda a surahn idonsa na kan qur'an din, duk yaran suka maida hankali kan qur'an din suma suna saurarensa, a aya ta bakwai suka ce masa Abbunsu ya tsaya masu, don haka ya dinga maimaita masu idanuwan su a kan qur'an din gabansu, har Abuturrab ya shigo parlon, tun daga bakin kofa yake kallonsu da mamaki har ya karaso inda suke, Mr David ya kai aya snn yace "Hope it's clear" duk suka gyada masa kai snn suka rufe qur'an din suka mike suna kallon Abuturrab suka yi masa sannu da xuwa da larabci suka bar parlon, xaunawa yyi kan kujera yana kallon Mr David yace "Ina yini Abba" Mr David ya kallesa yace "Lafiya Aliyu, sun sa sai na biya masu hadda" Abuturrab yyi murmushi yace "Baka mance karatun qur'an ba knn Abba" murmushi yyi bai ce komai ba ya mike yace "As usual i came to check on dem, sai next Friday" daga haka ya nufi kofa Abuturrab ya bi sa da kallo a sanyaye, ganin zai fita yace "Abba abinci fa?" Ba tare da ya juyo ba yace "Ohh Alhmdllh tnx" daga haka ya fita, Abuturrab ya kasa dauke idonsa a kan kofar. Tunda Mr David ya isa gida ya kasa shiga parlor yyi tsaye Balcony, ya rasa tunanin da yake, ganin har bayan minti talatin bai shigo ba Rachael dake parlor da kawarta ta aiki 'yar yayarta dake Ghana, warce aka bata madadin Samantha a cewarsu, tace mata taje ta duba me yake yi a waje, yarinyar da baxa ta wuce 20 ba ta dawo tace "Kawai yana tsaye ne Mumy" mikewa Rachael tayi ta fita ta tsaya tana kallonsa, can ta tabe baki ta koma ciki, bayan minti goma taji fitar motarsa gidan, Kawarta Esther tace "Mantuwa yayi ne?" Rachael tace "Who knws for him, na lura tunda aka ban Comfort yake bakin ciki, yaga na yaye yar sa a rayuwata, ni a ynxu da kika gan ni bani da ya a duniya da ta wuce comfort" Esther tace "Gaskiya kam, amma kina jin labarin samantha da yaran nata kuwa?" Rachael tace "Ynxun ma da kika gansa na san daga can yake, yaranta kuma yace min sun girma amma ni ba matsala ta bace wnn, comfort ce komai na ynxu" Esther tace "Anya kuwa David ba cewa xai yi shi ma xai koma musulunci ba" Dariya sosai Rachael tayi tace "Da kuwa ya gwammace ba mu hadu a rayuwa ba" tun daga wnn rana idan Mr David yaje gun grandchildren din nasa sai sun dauko masa qur'an ya biya masu, Noor na jin dadin hakan har ranta a ko da yaushe kuma fata take Allah yasa Abbanta ya dawo islam, da farko bai yrda ya dau qur'an din sai dai yasa su ajiye masa kan pray mat, daga baya kuma taga yana dauka. Ana haka su Arshaq suka yi long vacation xa su primary 3, tun kafin hutun Abuturrab ke tunanin kai su can gidansu su yi hutun, rabonsu da gidan tun suna jarirai, sun dai san paternal grandpa din nasu a hoto, a ko da yaushe kuma su kan tambayi Abban nasu yana ina, me yasa basu taba ganinsa ba, sai yaushe xa su gansa, labarinsa kam bbu wanda basu sani ba don Abban nasu na gaya masu about him, Abuturrab na son kai su gidan su ga Mahaifinsa amma yana tsoron abinda xai iya biyowa baya, shi dai ya kan je duk da har lkcn Abba baya sake masa, Da small Mum dinsa yyi shawarar kai su can gidan nasu su yi hutu ta kuma basa goyan baya dari bisa dari tace idan sun je sai a ga ko xai koro su, Ita dai Noor bata ce komai ba, boys din kam where very happy xasu gun kakan nasu, ranan lahadi Noor ta gama hada masu kayansu na hutun gaba daya har da takardun karatun su, suka dau hanyar gidansu Abuturrab, ita ke driving din, Abuturrab kuma na xaune bayan motar da boys din nasa yana kuma basu lbrin Col Ahmad, Arshaq ya xaro ido yace "You mean Gun Abbu?" Abuturrab ya gyada kai yace "Of course, but the gun is meant for only those dat commit crimes like arm robbers, and kidnapers" Ashraf yace "Ohh that sounds nice, do he still wear his army wears?" Abuturrab ya dan bude ido yace "I don't think so, buh you can ask him to show u the wears, of course i knw he will" Arshaq yace "Waow am so eager to see him dad" Abuturrab yace "But mind you, he doesn't understand Hausa or English, but only Arabia" Ashraf yace "That's weird, even the lingua franca?" Abuturrab yace "Yeaa" Arshaq yace "Buh Grandma do speak English" yace "Ohh yea, but my dad doesn't" Ita dai Noor bata ce masu komai ba, Abuturrab na kallonta ta madubi yace "Ummu ain't you interested with our conversation" a takaice tace "Buh you told me to be mute always while driving" Ashraf ya bude hannu yace "Abbu forget things easily" Abuturrab yyi murmushi yana shafa kansa yana son ce mata ta gwale sa gaban yaransa amma bai san da wani yare ba, turancin suna ji, Hausan ma suna ji, Larabcin ma ji suke, can dai a hankali yace "Alryt, i remember now" Har suka isa gidan Col twins din basu bar jefa ma Dad dinsu tambayoyi game da kakan nasu ba, A waje yasa Noor tayi parking, Ya bude motar ya fito, yan biyun basu sakko ba sai da suka manna ma momma dinsu kiss tayi murmushi ta rungumesu gaba daya tace "Ku yi behaving kan ku kun ji, Abbun ku ya mance bai gaya maku ba har da bulalan dukan yara idan suka yi misbehaving grandpa ke da shi, duk suka yi shiru suna kallonta Arshaq yace "But, is he going to cane us also?" Ta hade rai yace "I didn't communicate with English" Ashraf yace "Toh xai doke mu mu ma?" Tace "Ehh idan ku ka yi rashin ji amma, boys kar ku yi fada don Allah, barin kai Arshaq, duk wanda yyi fada a gidan baxae sake xuwa ba, maza ku bi bayan Abbu, ku gaida min grandma kima" ba musu suka sauka motar suka bi bayan Abban su, bbu kowa gidan ynxu bnda Ilham duk biyun sun yi aure lst yr, masu gadi Abuturrab ya hada da kayan boys din yace su kai masu ciki, su kuma yana kallonsu da larabci yace su bi bayansu kuma suce da Grandpa yana gaishe sa, duk sai yaga mood din su ya canxa ya duka yyi kissing dinsu a forehead yace "Grandpa will be glad seeing his grandboys, immediately you get in hug him nd give him a kiss before greeting him, go now" sake su yyi suka bi bayan soldiers din suna daga masa hannu, yyi murmushi ya mike ya koma gun mota, Mami ce ta fara ganin yaran ta fito daga kitchen, suna ganinta suka nufeta da gudu suka rungumeta suka ce "Grandma we came for holiday" sosai tayi farin cikin ganin jikokin nata ta rungumesu gaba daya tace "Ohhh Welcm my boys, ina Abbun naku" Ashraf yace "Ya tafi da Ummu" tace "Maa sha Allah, Ku xo ku gaida grand dad" daga haka ta ja su xuwa parlon col ta bar su nn bakin kofa tace su shiga, duk suka shiga parlorn da sallama, Col dake waya ya juya yana kallonsu, katse wayar yyi ya ajiye ya cire glass din idonsa yana kallonsu da mmki, duk suka karasa inda yake da gudu suka rungumesa a tare suka manna masa kiss a forehead da murnan su suka gaishesa da larabci kmr ynda Abbu yace masu, murmushi ne yyi escaping lips dinsa ya rungume su shi ma da larabcin ya amsa gaisuwarsu yana tambayarsu daga ina suke, nn suka fara yara masa, tun yana tsintar yaren yana gane abinda suke cewa har ya daina, dariya yyi sosai da turanci yace shi kam baya jin Arabia, Ashraf yace "Oops but Abbu told us u don't understand lingua franca, only Arabic" ya rungumo yaran yace "He is just pulling ya legs boys" nan suka dinga hira da kakan nasu with English, Arshaq ya dage sai ya nuna masu bindigarsa da kayan soldiers, shi kam murmushi kawai yake yace To xai nuna masu da daddare, Mami bata taba xaton Col xai ji da yaran kmr ynda yake ji da su ba, in dai ba fita me nisa xae yi ba to da su xai fita, in ko yana gida suna makale da shi suna masa shirme abinci ma tare yake ci da su, har ransa yake son yaran wnda ya kasa boye hakan, duk bayan sllhn asuba shi ke masu karin qur'an, tun da suka xo gidan bai taba ce masu su tashi su yi sllh ba sai dai idan bacci suke, da lkci yyi xa su yi alwala su tafi masallaci tare da shi, a tare yake kwana da jikokin nasa a bedroom dinsa, tsakaninsu da Mami sai dai tayi masu wanka ta shirya su, a haka har hutun su ya kusa karewa, shopping ba na wasa ba Col yyi masu, ana gobe xa su koma makaranta ya umarci driver da ya maida su gida, suka ce inaa sai dai Grandpa *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 103..... Duk ynda Col ya so yyi convincing dinsu Driver ya kai su k'in amincewa suka yi, hakan yasa ya shirya ya dau makullin motar sa, Mami da Ilham suka kai kayan boys din cikin mota, duk suka yi kissing Mami suka ce "We will miss you grandma" Murmushi tayi tace "I will miss you also boys" daga haka suka bude front seat xa su shiga ilham tace "Oh nice baxa ku yi miss ba ko?" Dariya suka yi Arshaq yace "Alryt cum closer" ilham ta karasa kusa da su ita ma suka yi pecking dinta suka ce "We'll miss you aunt" tace "Better" Col ya bude driver seat ya shiga Mami ta xagaya tace "You didn't ask for the Address col" ta gefen ido ya kalleta yace "Da yake ke kika siya fili gun kika gina gidan" yar dariya tayi tace "A'a ba sai an hada da baka ba ai" Tada motar yyi su Arshaq suka dinga d'aga ma Mami da ilham hannu har motar ya bar gidan, Ashraf yace "Grandpa would we be cumin here for our next holiday?" Arshaq yace "Yes grandpa, we love it in here" Col yace "It's left for your papa" suka yi shiru, Ashraf yace "We will convince him in sha Allah" murmushi Col yyi yace "But how old are my brave boys?" Arshaq yace "Ohh i am eight yrs old, while he is seven" ya karasa yana nuna Ashraf, naushi Ashraf ya kai masa ya hade rai yace "How dare you say u re older than me, we re of the same age grandpa" lallaba su Col yyi suka hakura, har dai ya isa gidan Abuturrab, Ashraf yace "Waow hw did you knw our dad's home grandpa" Col ya kallesa yace "He is my Son just as he is ur dad..." Arshaq yace "But for all this while why didn't you cum to see him" Ashraf yace "He once told us that u re angry with him, why is dat grandpa...." Murmushi kawai Col yyi yace "He lied" Arshaq yace "Noo our Abbu doesn't lie" bude motar Col yyi ya fita har lkcn murmushi yake, su ma suka fito ya fiddo masu tsarabar su, tuni mai gadin gidan ya karaso yana gaishesa ya amsa ya mika masa babban ledan hannunsa yace "Ka shiga da su" Arshaq yace "Grandpa ain't u cumin in with us" yace "Yes am nt" da damuwa Ashraf yace "But why?" Yace "Am in a haste u see" Arshaq da har ya bata fuska xai yi kuka ya koma cikin motar yace "Ni ma baxan shiga ba, i am going bck with you, Ashraf cum in" Ashraf ya shiga motar shi ma, dariya yaran suka basa ya dake yace "But.... Ohk ohk am sorry boys ku fito ku kira min Abbun naku am waiting here" Ashraf na nuna masa seven fimgers yace "Grandpa we re seven yrs old" dariya Col yyi yace "Meaning?" Yace "Xaka mana" Arshaq yace "Pls grandpa let go in togeda so u can meet our Ummu" Col dai rungume hannu yyi yana kallonsu, can ya ciro makullin motar ya karbi ledan hannun mai gadin ya nufi gate din, yaran suka fito da sauri suka bi bayansa ya rufe motar, su suka fara shiga parlon snn shi ma ya shiga, dai dai sakkowar Abuturrab kasa, tsaye yyi yana kallon Abban sa ya kasa karasowa cikin parlorn, yaran suka tafi da gudu suka rungumesa da Arabia suke ce masa sun dawo da grandpa, murmushi ya kirkira yace "Yea i saw him" daga nn suka rike hannunsa suka dawo parlon gaba daya, Arshaq yace "Abbu, grandpa denied being angry with you, he said he is nt" Abuturrab yyi tsuru yana kallonsu, can ya kalli Abban sa da ya kasa boye murmushin sa, ya xauna kansa a kasa yace "Ina kwana Abba" Col yace "Alhmdllh" Arshaq yace "Abbu we love ur dad" murmushi yyi yana gyada kai, can ya mike yace "Bari in kirata Abba" daga hka ya wuce sama, Ashraf ya tafi fridge ya dauko ma grandpa din nasu ruwa Col ya karba yana murmushi ya manna masa kiss a goshi yace "Thank my boy, ba ku je kun gaida mum ba" Ashraf yace "Xaka wuce idan muka je upstairs" Kwance Abuturrab ya tadda Noor, yyi tsaye bakin gadon yana kallonta, can ya xauna ya kai hannu fuskarta a hankali yace "Wife" bude ido tayi yace "Ur boys are back, ki daure ki xo ku gaisa da Abbana" ta mike xaune tace "Da gske?" Yace "Yea wife" hijab ta dauka suka fita a tare, nesa da Col Noor ta durkusa ta gaishe sa, ya amsa yana tambayarta gida, su Arshaq suka tafi suka rungumeta suna cewa "Ummu mun dawo, Grandpa is very lovely" murmushi kawai tayi bata ce komai ba, Col ya mike yana kallon yaran yace "Hope i am free to go now" suka koma gunsa suka yace "Yea grandpa, we wish to spend our next holiday with you" dubu goma ya ciro aljihunsa ya damka musu dubu biyar biyar, da farko kin karba suka yi har sai da Abuturrab yace su karba, snn Col ya bar parlon bayan Noor tayi masa Allah kiyaye, yan biyun kuma na daga masa hannu, Abuturrab ya bi bayan Abban nasa, Arshaq ya dago kan Noor yace "Ummu are you sick" tayi murmushi tace "Why did u ask?" Ashraf yace "You look pale" tace "I am getting better now" mikewa tayi ta wuce sama da boys din nata. Da daddare Noor na kwance Abuturrab ya shigo dakin bayan ya samu su Arshaq sun yi bacci don tun dawowarsu suke ta basa lbrin holiday din su, da abubuwan da Abbansa yyi masu, da wajajen da ya kai su, ya cire duvet din jikinta yace "Tun da baki son allura ga drugs na siyo maki" tace "Ni nace maka i don't need anything, i will be fine" yace "Kin ga fa xan kira mum in hada ki da ita, you've being sick tun shekaranjiya kin ki yrda ki sha magani" kallonsa tayi tace "Toh fa na ce maka i will be fine" ya kamo hannunta yace "But ni baki taba rashin lfya na baki magani ki ki sha ba wife, tell me what ur problem is" mikewa xaune tayi tace "My problem is baxa ka sake xubar min da ciki ba" daga haka ta sauka kan gadon ta nufi kofa, ya bi ta da kallon mamaki har ta fita, lkci daya jikinsa yyi sanyi ya kuma ji kunya ba kadan ba, dafe kansa yyi na kusan minti biyar, can ya dago ya mike ya fita dakin, wani bedroom daban ya sameta duk ya kasa barin su hada ido ya xauna yace "Am sorry Noor, but it's nt my fault" tace "It's mine then" ya girgixa kai yace "No baby, i have my reasons for Aborting ur pregnancy" bata ko kallesa ba yace "Ki yi hakuri don Allah" tace "Nayi amma ni baxa ka xubar min da ciki ba" yace "I have to dear, ba kuma da son raina xan yi haka ba" tace "Toh sai dai ka kashe mu baki daya" rasa abinda xae ce mata yyi, can ya mike ya fita daga dakin. Washegari da safe shi ya yi ma boys dinsa wanka ya shirya su cikin uniform dinsu, ya hada masu shayi da bread nd butter, suna gamawa ya dau makullin mota xai ajiye su schl, Arshaq yace "Abbu we've nt seen ummu" Ya shafa kansa yace "She's still sleeping" Ashraf yace "Can we go in and see her" sake su yyi yace "Alryt" duk suka shiga bedroom dinta, tana kwance idonta biyu suka karasa kan gadon duk suka gaisheta tace "How r you two" Arshaq yace "We are fine, Abbu told us u were sleeping" ta gyada kai tace "I just woke up" daga haka tace su tafi kar su yi late, suka daga mata hannu suka bar dakin, ko da Abuturrab ya dawo daga kai su makaranta Noor na daki har lkcn, sai da ya gama shirin fita aiki snn ya shiga dakin sai tayi kamar bacci take, hakan yasa yyi wucewarsa kawai, yana office ranan Hajiya Mariya ta kirasa, bayan sun gaisa tace idan ya tashi office ya biyo gidanta, murmushi yyi bayan ya ajiye wayar don yasan sauran, ae kam yana xuwa gidan da yamma abinda ya xarga ne ya faru, ya jira ta gama fadan ta snn yace "Amma mum kin san ynda muka yi da Abba da yakumbo" tace "Aikin bnxa kafi tsoronsa a kan ubangijin ka knn..." Shiru yyi bai ce komai ba. Laulayin da yafi na cikin su Arshaq wahala Noor ke yi, duk ta fita hayyacinta, gashi ko wani irin taimako xai bata na medication nunawa take bata so duk ta ki yrda da shi, hakan yasa Hajiya Mariya tasa wata kawarta likita ke xuwa gidan dubata tana bata medication ynda ya kamata don ita ma ba yrda da shi tayi ba, Abuturrab kam ya xama d'an kallo, yaran biyu duk Hajiya Mariya ta maida su gunta, Ilham ce ta xauna da ita tana taimaka mata aikace aikacen gidan, kafin watanni hudu Noor ta fara samun kanta har lkcn ko paracetamol bata yrda ta sha idan Abuturrab ya bata, sosai take kewan yaranta da Abbanta, don tunda Hajiya Mariya ta tafi da su shi ma ya daina xuwa, ana haka har watan haihuwar ta ya tsaya, ita fa har xuciyarta bata yrda Abuturrab ya amshi haihuwarta ba kuma kiri kiri ta gaya masa, ya saki baki yana kallonta, can yace "Ko sbda me?" Tace "Haka kawai ka kashe min baby tunda ba so kke ba" bai ce komai ba don bai ji ddin hakan da tace ba, har ta mance da xancen yace "Toh ko na kashe babyn ai nawa ne" bata kallesa ba bare ta tanka sa, ranan da ta fara nakuda axaba yasa ta mance da abinda ta fada masa na cewa kar ya xo kusa da ita idan xata haihu, kuma a gida da taimakonsa ta haifi tsalelliyar yar ta mace daren friday, bbu abinda babyn nn ta mance na Noor kmr tayi kaki, don har ta fi yayinta maza kyau ga hanci maa sha Allah fara tass da ita, farin cikin da Abuturrab yyi a daren nn ba a magana, sai da ya kintsa su yana murmushi yace "Toh gashi har ke ke cewa in taimake ki wife, sai naji baki ce aje asibiti ba" kunya ya kamata ta dauke kanta tace "Ni bn ce haka ba..." rungumeta yyi ya lumshe ido yace "Gaskiya baby kina da dauriya ssai, haka kika yi da xaki haifi su Arshaq?" Tace "Ka tambayesu xa su gaya maka" ya ja hancinta yace "Kin san carbon copy dinki ne a cikin ki shi yasa kika dage sai kin haifeta ko" murmushi kawai Noor tayi tana kallon cute babynta dake bacci. Ranan suna dai Baby ta ci sunan Ummin Gombe wato Hajarah, tun ana gobe suna Anty Maryam ta xo gidan, abun mamaki har da Yakumbo a xuwa sunan fa, su Arshaq suka sa ta gaba kamar yanda Hajiya Mariya tace masu ai ba fa ta jin ko wani yare bnda larabaci a duniya, nn suka dinga yara mata tana kyalkyala dariya uwa tana jin abinda suke cewa, nan kuwa ji take kamar an sa ta aljanna jin yaren da jikokin nata ke mata da fararen jallabiyarsu da hula, Kaya ba na wasa ba Ummi ta taho ma da takwararta me kyau, Ummar su Ahmad da yaranta mata gaba daya suka xo sunan su ma, aka yi suna na gani na fada aka watse lafiya, kaya ba na wasa ba babyn ta samu, sai bayan suna da sati daya ko me Col ya gani sai ga shi ya xo ganin 'yar matar tasa me kyau, dubu hamsin ya ajiye ma babyn da ake kira da *Noorul Huda* Abuturrab yaji ddin xuwan Abban nasa. Bayan suna da wata guda Abban Noor ya taho ganin matar sa shi ma. Little Noor na da wata Huda su Arshaq suka kuma samun long Vacation, murna suka yi tayi suna jiran jin inda Abbunsu xai ce xa su for the holiday, Noor na bedroom dinta tana shirya little Noor Abuturrab ya shigo dakin, xaunawa yyi kusa da su yana jan Cheeks din daughter sa yace "Ummu am thinking Boys din su je Holiday gun mum, i mean ur Mum" dago kai tayi tana kallonsa ya buda ido yace "Yea, it's nothing wife, naga yaran na da wayo sosai kuma ai Abba na gidan" bata ce komai ba ita dai ya dau little Noor dake masa dariya ya mike yace "Sai ki hada masu kayansu" daga haka ya fita daga dakin, Noor duk jikinta yyi sanyi don ita kam tsoron mum dinta take ynxu. Daki Abuturrab ya samu su Arshaq suna hada bricks, ya xauna duk suka dawo kusa da shi yace "You two are going to ur grandma's place for the Holiday!" A tare suka ce "which?" Yace "Your Ummu's mum" Xaro ido Arshaq yyi yace "Waoww, but ummu once told me she's nt like us, i didn't get what she meant then, is it that she is not Human?" Ashraf yace "Yeaa i also remembered Ummu saying that" Abuturrab yace "Noo, she is Human like us..." Arshaq yace "But Ummu have never for once said she is going to her mum's place" Abuturrab yace "It's because her mum is angry with her just as my dad was with me sometimes ago" Arshaq yace "That's strange, why are ur parents both angry with you?" Abuturrab da yaji tambayar har tsakar kansa yace "I think we need to close that chapter now, and as i was saying, i knw Ur Mu'allima's and Mu'allim's have taught you what is prohibited nd accepted in Islam, i want you two to abide by it while in Grandma's place. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 104...... Kamar wancan lkcn Noor ce ke driving din sai dai gaba daya hnklinta bai jikinta, Abuturrab kuma na xaune da yaran nasa uku a bayan mota, Baby Noor na kafarsa su kuma suna gefensa, Arshaq ne yyi breaking silence din yace "Abbu, will grandma be happy seeing us?" Abuturrab ya ja hancinsa yace "Of course my boy, she will be very very happy" Ashraf yace "Are we going in alone?" Abuturrab ya shafa kansa yace "Yes boy, lastly i want you two to behave ur self while with grandma" kai kawai suka gyada masa, suna isa gidan Noor tayi parking tana kallon Abuturrab, ya sakar mata murmushi ya mika mata Baby Noor ya fita daga motar don ciro kayan yaran a bayan mota, Noor na kallon twins dinta tace "Kar ku yi ma Grandma rashin ji xata yi caning din ku, kuma bata son surutu dayawa ko kuma ku fadi abinda ba a tambaye ku ba, kuma ku ce da grandpa ya dinga k'ara maku karatu" Duk suka ce "Ohk Mum" 'yar kanwarsu me kyau suka yi ma kiss suka sauka daga motar ta bi su da kallo tana murmushi, Mai gadi Abuturrab ya ba kayansu yace ya karasa da su ciki, suka rungumesa suka ce "We wil mis u Abbu" Yace "I will miss my children also" daga haka ya mike suka bi bayan mai gadin. Comfort ce kadai kwance parlon tana kallo, suka tsaya suna kallonta kamr ynda ita ma ke kallonsu, Arshaq yace "Good afternoon," ta mike xaune har lkcn tana kallonsu, Ashraf ya kalli d'an uwansa yace "That's strange, i don't think she understands English" dai dai fitowar Rachael daga kitchen tana cewa "Gashi can kije ki debi abincin na gama" kallon gun da Comfort take kallo tayi ta ga yaran tsaye, sai ita ma ta tsaya kallonsu, Arshaq ya karasa parlon yana kallonta a hankali yace "Sorry plss, are u our grandmum?" Rachael tace "Jesussss christ of Nazareth, Comfort these are Samantha's Children, they are her boys" Arshaq ya kalli Ashraf da ya karaso ciki shi ma murya can kasa yace "May be Ummu nd Abbu mistook this to be d house" Rachael ta karasa da sauri ta rungumosu cikin mugun farin ciki tace "Yess my boys i am ur grandmum, this is me, who brought you two here?" Ashraf yace "Our Mum nd Dad" ta kalli kofa da sauri tace "Where are they?" Yace "They are gone, they brought us here for holiday" rungumesu ta kuma yi tace "You are welcm my children, you are welcm, you re welcm" Daga haka ta ja su xuwa sama baki har kunne tana cewa "I am ur grandma children, i gave birth to ur mother" Dakinta ta shigar da su ta xaunar da su kan gado tace "Let me get you two something" tana fita dakin Arshaq yayi tagumi, bayan mintoci yace "I don't think i will like it in here" Ashraf dake ta kare ma dakin kallo yace "Why did u say so?" Shigowar Rachael yasa Arshaq bai ce komai ba, ta mika masu lemo a glass cup suka karba ta xauna gefensu tana washe baki tace "So what shuld i cook for my twins" Ashraf yace "Noodles.." Ta kalli Arshaq tana shafa kansa tace "And you boy?" Yace "Same" tace "Do you take it with egg?" A tare suka gyada mata kai ta mike ta kunna masu TV tace "Let me get it right away for you two" daga haka ta fita, Arshaq ya dau remote ya maida channel din xuwa na Cartoon. Bayan minti sha biyar sai ga Rachael ta shigo da plate na Noodles Comfort na biye da ita da wani plate din ko wanne da kwai uku a kai, ta ajiye masu kan Carpet tana kallonsu tace "It's ready boys" sakkowa suka yi kasa, Comfort na murmushi tace "Welcm boys" duk suka kalleta suka ce "Thank you" Rachael ta xauna ita ma tana kallonsu cike da so har suka fara cin abincin, tace "I am still yet to knw d names of my handsome boyss" Arshaq yace "Grandma talking while eating is a bad table manner..." ta wara ido tace "Ohhh dats very true love" Comfort ta xauna gefen gado tana murmushi, Rachael bata kuma ce masu komai ba sai tagumi da tayi tana kallonsu, wai ynxu kyawawan yaran nn yaran Samanthar ta ce, ita ta haifesu, ta lumshe ido tace "Thank you lord jesus for providing me with this lovely kids into my family, father God i commit them into ur holy hands, nd i cover every part of dem with d blood of jesus" daga Arshaq har Ashraf sake baki suka yi suna kallonta, can Arshaq ya xaro ido yace "What r u doing grandma?" Ta bude ido da sauri tace "Am praying for you sweet kids" Ashraf ya ajiye fork din hannunsa yace "That's odd...." Xata yi magana wayarta yyi ringing ta mike da sauri ta dauka taga Sarah ce ke kiranta tana dagawa cike da farin ciki tace "Sarah yau ga yan biyun Rebecca sun xo min hutu" daga daya bangaren Sarah tace "Haba Sister?" Rachael tace "Am telling u Sarah, ki xo ki gan su" Sarah tace "toh gani xuwa" daga haka ta katse wayar ta fita dauko ma jikokin nata ruwa tana murmushi, ana gama kiran La'asar Twins din suka mike daga gun abincin, Rachael tace "Ba ku cinye ba ai yarana" Arshaq yace "We are full" Comfort ta hade abincin waje daya ta fita da su, Ashraf yace "Grandma we want to perform ablution" daga sama har kasa take kallonsu can tace "We don't do that here...." Arshaq yace "i dnt get you?" Ta mike tana xaro masa ido tace "Ga cartoon ana yi kuyi kallon ku" Ashraf yace "But it's time for prayer" Arshaq ya nufi kofar da yake tunanin toilet ne ta rikosa tace "Kai cikin sanyin nn xaka xuba ruwan sanyi jikin ka, do you want to catch cold" ganin ynda yaran suka tsaya kallonta ta d'an bata fuska tace "Ai shknn bari in sa maku ruwan dumi, amma ni bni da kettle a gidana" Ashraf yace "But why is that, didn't you use to pray?" Ta rike kugu tace "I dnt pray d way u pple do, it's very wrong" toilet din ta shiga ta xuba masu ruwan dumi a bowl ta dawo tace su je su yi alwalan, ba musu suka shiga toilet din su biyu, ta xauna tayi tagumi tana kada kafa, wato har sun cusa ma yaran nn musulunci ko, to baxa ta sa6u ba, tana kallonsu suka fito suna dube duben darduma, Arshaq yace "Grandma praymat?" Tace "I've told u pple i dnt pray d way u do" A tare suka ce "Then hw do you pray" durkusawa kasa tayi ta hade hannayenta ta rufe idonta ta shiga kwararo addu'ar coci tsakaninta da Allah, Suka fashe da dariya ta bude ido tana kallonsu Arshaq yace "That's weird, i think that shud be d barbarians way of worshipping, it's just strange, that's not hw islam teaches us to pray to Allah" Ashraf yace "Anyway, where can we find d nearest mosque grandma" sake baki kawai tayi tana kallonsu, can ta mike ta hade rai sosai tace "yanda kuke naku addu'ar ne kalan na babarians, c'mon ku wuce ku xauna bbu inda xa ku fita, you two are going no where, ga cartoon nn na sa maku" Arshaq yace "I said it, i knw i will never like it here, am gonna give dad a call ryt away to cum take us away from this goddam home, am nt staying any longer...." yana magana ne kamar xai yi kuka, Ashraf ya rungume hannayensa ya juya baya yace "Yaa Allah" Rachael ta karasa da sauri ta rungumo Arshaq jin furucin sa tace "No, no don't say that son, u will like it much here, grandma loves you a lot, dnt wrry let me escort u two to d mosque" daga haka ta kama hannunsu ta fita dakin da su, Comfort na tambayarta inda xata bata tanka ta ba har suka fita gidan, masallacin unguwar ta kai su suna shiga ta nemi wani dakali nesa da masallacin ta xauna tana jiransu, kowa ya xo wucewa sai ya kalleta, har aka idar da sllh sai gasu sun fito, suka taho gun ta, Arshaq yace "Ohh you waited for us grandma" ya manna mata kiss a goshi yace "I love you Grandma" rungumesa tayi tace "I love you my handsome" daga haka ta mike ta kama hannunsu ta dau hanyar gida duk aka bi su da kallo, daren ranan da Mr David ya dawo shi ma ba karamin farin cikin ganin jikokin nasa sun xo hutu gidansa yyi ba, yaran suka ji ddin ganinsa sosai su ma, a kwanakin yaran biyu a gidan David har mamakin matar tasa ya dinga yi ynda duk abinda yaran suka nuna suke so shi take yi masu ko da kuwa na addinin islam ne, ji take kmr ta mayar da su ciki don so, bata sake gigin kkrin hana su yin sllh ba, church kuma tun da ta kai su suka dinga rusa mata kuka su gida xa su koma bata sake kai su ba, Rosary ma da ta sa masu suka nuna basa so bata sake sa masu ba, in dai Mr David bai nn ita ke raka su masallaci yin sllh, har tanadar masu ruwan alwala take a flask, ko kadan bata son bacin ran jikokin nata, yaran suka saki jikinsu sosai a gidan, suma kuma sosai suke sonta kamar yanda take son su, ita ke coaching dinsu a karatun bokonsu, kullum dare kafin su kwanta sai sun yi karatun qur'an, wani lkcn ta xauna ta sa su gaba tana kallon ikon Allah ba dai dama tace baxa su yi ba su tada mata bori in dai su yi bacci ta kan dauki bible ta sa a tsakankaninsu, duk gidan kawayenta sae da ta bi ta nunnuna su, har addu'a take kar hutun ya kare don yaran sun yaye mata bakin cikin da ke kunshe a xuciyarta na shekara da shekaru, ana saura kwana biyu xa su koma makaranta kuwa bbu abinda ta mance bata siya masu ba, Mr David ke driving din ranan lahadi xa a maida su gida, Rachael na xaune bayan mota da yan biyun, Ashraf yace "Am seriously going to miss u grandma..." Ta jawo sa jikinta da damuwa tace "will miss u also prince" Arshaq yace "Grandma ki dinga xuwa gidanmu plsss" Tace "I can't withstand d sight of ur mother" Ashraf ya kalleta yace "Why?" Ta tabe baki tace "I just don't want to see her" Ashraf ya janye jikinsa a nata, Arshaq yace "But where did she she wrong you?" Rachael tace "When u get home as her" shi dai David bai ce komai ba, har suka isa gidan bbu wanda ya sake cewa komai, Ashraf ya bude mota xae fita, Rachael ta rikosa tace "Without even a goodbye my prince" ya hade fuska yace "Not when u can't withstand d sight of my mother, i will neva spend my holiday with you again" da damuwa tace "Nooo, Am sorry prince, may be i shud'nt have said that...." Yace "Then cum in nd meet my mum" Arshaq yace "Yess plss, and little Noor also, she's so beautiful grandma, i knw u will love her" Rachael dai sai kallonsu take, Ashraf yace "You're nt cuming right?" ajiyar xuciya ta sauke tace "Alryt" daga haka ta fito tana kallon Mr David dake ta murmushi, ta hararesa ta bi bayan yaran dake jan ta xuwa cikin gidan nasu. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 105..... Babu kowa parlon sai Tv dake a kunne, Noor dake bedroom dinta da little Noor ta fito jin an bude kofar parlor, dakin Abuturrab ta leka ta gansa xaune yana operating laptop ya dago ya kalleta yace "Someone is at d door" bata ce komai ba ta sauka, kasa karasawa parlorn tayi ganin Mum dinta tsaye, Arshaq da Ashraf suka taho da gudu ganinta suka rungumeta suna cewa "We re back sweet mum, our holiday was superb with grandma" Rachael kam sai wani kallo take mata na tara saura qtr, Arshaq ya ja hannun mum din tasa yace "Ummu we came with grandma" Noor sai kirkiran murmushi take ta karasa parlorn Ashraf ya karbi little Noor ya kai ta gun Rachael yace "Take a look at our little sis grandma" Rachael ta karbi yarinyar da ta fara bata fuska xata yi kuka, kallonta kawai Rachael ke yi don sak Samantha tana karama, xaunawa tayi kan kujera har lkcn tana kallon Noorul Huda, Arshaq yace "Isn't she cute?" Murmushi Rachael tayi tace "Yess she is" Arshaq yyi peck din kanwartasa yace "Little Noor meet grandma for d 1st time, she's d best, she took very good care of us during our stay with her" Ashraf yace "Ummu, Grandma came to see u, go to her" Rachael ta daga hannu da sauri tace "Noo, noo i came to see my little angel" Arshaq ya bata fuska yace "With mum also" Rachael ta kirkira murmushi tana shafa kansa tace "Yes Prince" da kyar Noor ta xauna kasan carpet tana kallon Uwar tata tace "Ina yini Mum" Ba tare da Rachael ta kalleta ba tace "Eh lafiya lau" Abuturrab ne ya sakko parlon jin muryan kids din nasa, ya karaso parlon yana kallon Mum din Noor ya dai yi karfin halin cewa "Ina yini mum" ta kallesa ta watsa masa harara tace "Lafiya lau" Mikewa Noor tayi ta tafi fridge dauko ma mum dinta ruwa, Rachael kasa barin gidan tayi sbda jikokinta, duk da taki sake ma Noor bare Abuturrab fuska, gaba daya su Arshaq na xagaye da ita da yar kanwarsu da Rachael taji kmr ta gudu da ita amma ba dama, ji tayi dama ta dauwama har abada tare da yaran sbda so, su suka tilastata ta ci lunch din jollof din Cous Cous da yaji kayan hadi wanda Noor ta yi, sai kusan karfe uku ta bar gidan, bbu ynda Abuturrab bai yi yyi dropping dinta ba amma taki yrda don tuni Mr David ya wuce, wannan ne mafarin fara kiran Abuturrab da Rachael tayi bayan ta karbi numbersa gun Mai gidanta, kusan kullum sai sun yi waya da yan jikokin nata, wani lkcn Noor kan karbi wayar ta gaisheta duk da ba wani amsawan kirki take mata ba amma tana jin dadin yanda take ji da grandchildren dinta, bayan duk sati biyu ta kan xo gidan ranan asabar amma iyakarta balcony ta ba yaran abinda xata basu tayi wucewarta, hakan yasa Noor ta fara kwadayin xuwa gida ko da kuwa da yaran ne, kilan sanadin hakan su samu masalha da mahaifiyarta, hakan kuwa aka yi ranan wata friday Noor tace da Abuturrab tana son xuwa gidansu tayi weekend da kids din nata, da kansa ya kai su gaba daya gidan, har ya shiga ya gaida mum din shi ma, Rachael tayi murnan xuwan su har ita Noor din amma a fili nuna cewa murnan xuwan yaran kadai tayi, bbu abinda ta rage su da shi, duk da fa magana me tsayi bata yrda ya hadata da 'yar tata, ranan lahadi da safe Noor na daki tana bacci Rachael ta shigo tana tafe hannu tace "Toh nonbelievers ni dai xan wuce church, ga yara can basu tashi ba ki dinga kula min da su har in dawo, idan kuma suka tashi ga breakfast na hada masu a kitchen, wankan ma ba sai kin masu ba xan masu idan na dawo" bata jira cewar Noor ba ta fita, Noor tayi murmushi ta koma ta kwanta, a yammacin ranan little Noor ke ta xaxxabi Rachael duk ta rikice nan ta samo Rosary ta rayata mata a wuya, Noor dai ta kasa cewa komai kuma bata cire ba, Arshaq na kyalla ido ya gani ya cire yana cewa "Grandma am begging you plss don't put this on our little sis again, it's a burden" Rachael da ke ta kallonsa ta kwace abarta tace "Alryt give it to me" daga haka ta bar masu parlon, Noor tayi murmushi tana kallon Arshaq da ya koma ya ci gaba da kallonsa, hka suka karashi weekend din a gidan Abuturrab ya xo da daddare ya daukesu suka koma gida. Bayan sati biyu sai ga Sadeeq ya kawo ma Abuturrab Katin aurensa, Abuturrab ya taya sa murna sosai yace "In ji dai Zainab ce?" Dariya Sadeeq yayi yana rungume da Namecy dinsa Arshaq yace "Yea ta ci sa'a ita ce" Abuturrab ma yyi dariya yace "Ka dai ci sa'a" Sadeeq yace "Assiddiq nake son ka bani yyi mata xaman daki" Abuturrab na shafa kai yace "Na baka" Sadeeq yace "Am jet serious fah, ita kuma little Noor ina nan ina jiran girmanta kishiyar Zainab ce tun yanxu ka ji" Abuturrab ya wara ido yace "Me xata yi da tsoho?" Da yammacin ranan Abuturrab yasa sadeeq ya rakasa kasuwa ya siya bike sabuwa dal, Sadeeq sai mamaki yake bai dai ce masa komai ba sai da suka bar kasuwar yace "Kai kuma me xaka yi da bike frnd?" Abuturrab yace "Mu je kai dai kaga, dama kai nake jira ka xo" a gate din wani gida Abuturrab ya tsaida bike din ya sauka Sadeeq ma ya sauka, Abuturrab dai sai kallon gidan yake, yana kkrin tura d'an gate din gidan wasu matasa biyu suka fito, Abuturrab ya kare ma wanda ke facing dinsa kallo daga sama har kasa snn yace "Ka gane ni kuwa?" Mutumin na gyada kai yace "Kwarai kuwa na gane fuskar nan" Abuturrab ya kama hannunsa ya sa masa makullin bike din yace "Ga Machine dinka na dawo maka da shi, so srry for the inconvenience" kallonsa kawai mutumin ke yi ya kasa cewa komai, har Abuturrab ya juya xai wuce mutumin yace "Nagode kwarai da gaske" Sadeeq dake ta jinjina lamarin yace "Tab ai in nine tuni na mance, sai dai in biya sa a aljanna" dariya duk suka yi mutumin yyi exchanging Number da Abuturrab ya rakasu suka hau tricycle xa su koma gida, washegari Sadeeq ya koma Uk, don can yake rayuwarsa. Noor na shirin kwanciya Abuturrab ya shigo da Huda dake bacci ya kwantar da ita kan gado, ya karasa kusa da wife din tasa ya rungumota ta baya ya lumshe ido yace "Kinsan me Ummu?" Tana kallonsa ta mirror tace "Sai ka fada Abbu" jan hancinta yyi yace "Xa mu je Convocation din fatima Gombe" Bata ce komai ba bata sake kallonsa ba kuma ta shiga kkrin daure gashinta, ya karbe ribbon din yace "Am talking Ummu" still ba tare da ta kallesa ba a takaice tace "I don't think am going, baxan je ba" yace "But why? Naga kids din na midterm break ranan" A d'an fusace tace "Toh ku je mana ni baxan je ba" murmushi yyi sosai yace "Har bikin nata knn, cos an gama convocation din da kwana biyu bikinta" sai a snn ta kallesa, can kuma tace "Toh Allah ya kai mu, wa xata aura?" dariya yyi yace "Baki ji kunya ba Samhata?" Murmushin tayi ita ma tace "Kunyar me?" Yace "Kin fini sani" ta juyo ta wara masa ido tace "Ohh baka son ina kishin ka knn?" Lumshe ido yyi yace "So kai" ta rungumesa tana murmushi tace "Yauwa Abban twins dina" shirye shiryen xuwa gomben suka dinga yi, ranan talata kuwa suka dau hanya bayan sun je sun ma iyayensu gaba daya sallama, Noor bata wani yi mamakin cewar Dr Shariff ne angon fatiman ba, suna gombe har bayan bikin da kwana biyu, Noor bata so hakan ba don kids dinta xa su yi fashin makaranta knn, ranan Monday suka sallami Ummi, Ummi tace "Anya takwarata xata kuma bin titi kuwa Son, gaskiya k'ura yyi yawa" Rabi'a dake parlon ita ma tayi dariya tace "To Ummi ki biya mata jirgi kawai" Ummi tace "Ae hakan ma xa ayi, nawa ne flight din, daga baya sai ka xo ka dau motar ka" dariya Abuturrab yyi yace "Mami ba gida xa mu direct ba ma" Tace "Ina xa ku?" Ya shafa kai yace "Xa mu biya gun wani frnd dina ne" Ummi tace "Toh shkkn, Allah ya tsare" duk ynda Ummi ta so su karbi kudin da ta ba takwararta a cewarta Abuturrab bai yrda ya karba ba, a hka suka bar gidan, Noor dai na bayan motar da yaranta dake ta game da wayar Abbun su, ganin ba hanyar Kano ya dauka ba tace "Abbu ina xa mu kuma" ta madubi yake kallonta yace "Ziyara Ummu" tace "Kai Abbu my kids r missing classes fa" yace "This the only opportunity we have wife, baxa mu dawo garin nn lkci kusa ba" tace "Buh nan da wata hudu ae bikin khadija" Yace "Duk da haka dae Ummu" bata kuma cewa komai ba, sai da suka yi tafiyar kusan minti talatin snn ta d'ago inda xa su, tace "Kai dear hw did u want this kids to cope there? Kasan ba sabawa suka yi ba" yace "Ke lkcn kin san xa ki iya copying a can? Gun da har muka samu shelter for good two days ba wajen rainawa bane madam" ta xaro ido tace "No don't misunderstand me dear, i mean they r nt familiar with place like dat" yace "Yea, experience is the best teacher, let dem go nd learn, beside tun da mum dinsu ta hakura da rice during that time su ma xa su hakura ne ynxu" murmushi kawai tayi bata ce komai ba, ya kashe mata ido yana kwaikwayon muryarta yace "Baxan iya ci ba Dr..." Hararansa tayi ta rufe fuskarta, yyi dariya sosai yace "Eh mana, then na tambaye ki to me xa ki ci wai wani *Rice* ke ga baturiya" bata san lkcn da ta fashe da dariyar ba itama tace "Wayyo bana so dear ka bari plsssss" ya wara mata ido yace "Ae sae ma yaran ki sun girma na basu lbrin" kallon kids din nata dake ta playing game tayi tana murmushi. *Haske writers asso* 💫 *Noorul Huda*💫 By khaleesat Haiydar📚✍🏻 106..... Har mamakin ynda Abuturrab bai mance hanyar garin Noor ta dinga yi, suna isa Rugar dai dai kofar gidansu Alto Abuturrab yyi parking, ya fito daga motar yana kare ma gidan kallo, Arshaq sai damun Ummun sa yake ina ne nn Abbu ya kawo su tace "We came for visit son" Noor ta fito motar rike da little Noor, twins din suka ki fitowa motar ko wannensu ya tsuke fuska, Noor ce tayi sallama kofar gidan taji muryar Mama Hansai na amsawa daga ciki, a hankali ta sa kafa ta shiga gidan, Hansai dake sauke sanwan rana na dumamen tuwo daga kan wuta ta mike da sauri tana kallonta, murmushi Noor tayi ta isa kusa da ita ta durkusa tace "Sannu mama" Hansai ta saki salati tana tafe hannu tace "Wa xan gani haka, yar nan kuna duniya ashe, Allah mai girma sannun ki da xuwa, sannu da xuwa" da sauri ta shimfida mata tabarma tana yi mata sannu da xuwa cike da farin ciki ta karbi Noorul Huda snn Noor ta xauna tace "Mama bani daya bace yana waje" Hansai tace "Wai yayan ki? Allah sarki ce mashi ya shigo maxa maxa, Alto ma na kewaye Allah ya rufa asiri bai fita ba, ce ya shigo" Noor tace "Toh mama" ta mike ta fita waje, Abuturrab na tsaye jikin mota ya rungume hannayensa tace "Ku shigo dear" daga haka ta juya ta koma ciki, ya bude bayan motar yana kallon su Ashraf yace "Come down" Arshaq ya girgixa kai da sauri yace "Noo Abbu we will wait for you here plss" hade rai yayi yace "I will knock you both, get down immediately now" fitowa suka yi da sauri yace "It's a promise, here will be ur next place for holiday" duk kallonsa kawai suke basu ce komai ba, ya shiga gidan suka bi bayansa, Hansai ta rasa inda xa ta sa su gaba daya don farin ciki ta ciko masu kwarya da ruwa ta kawo tana ta yi masu sannu da xuwa, Alto ma ya fito bayi ya dinga masu lale marhaba yana washe baki, ya rungumo su Arshaq yana masu fillanci duk suka tsura masa ido, yayi dariya sosai yace "Ga shi dai da ganin ku an ga fulanawa amma bakwa ji" Murmushi Abuturrab yyi a xuciyarsa kuwa yace dole ma ya fara yi masu yaren, Alto yace "Toh Maa sha Allah, Allahu ya raya ku 'yan samari, ashe dai da rabon xa mu sake saduwa Ali, Allah mai girma" Abuturrab yace "Wllh kuwa Baffa, da fatan mun same ku lafiya" Baffa yace "Alhmdllh, Alhmdllh mun gode Allah, duk lfya lau muke wllh" yana son tambayar Binta amma shakkar Noor ya hana yyi hkn, yana ta jiran ita tayi tambayar amma ta ki, Hansai ta dauko kwano tana cewa "Wllh gashi ynxu na sauke dumamem tuwo da miyar kuka sai dai ko k'ashi bbu a miyar sai waran mu ta fulani da na jefa ciki, kuyi hakuri don Allah" Noor tace "Haba Mama ba komai mun ma ci abinci fa kafin mu fito" Hansai tace "A'a ni dae bara in xubo ku ci don Allah" daga haka ta xuba masu tuwon da miya a kai ta ajiye ma Noor da su Arshaq, Abuturrab ma ta xuba masa ta kai masa, murmushi yyi yace "Godiya muke mama" Wata kyakkyawar yarinya ce da baxa ta wuce shekaru 5 ba ta shigo gidan da 'yar karamar tulu a kanta, fara ce sosai gashinta har kusan gadon bayanta, ta ajiye ruwan kanta tace "Inno gashi na debo" Sai a snn Noor tace "Mama Binta fa?" Hansai ta kalleta sai dai bata ce komai ba, Alto dake xaune kusa da Abuturrab yace "Ae Binta Allah ya mata rasuwa shekaru biyar kenan" Noor taji xancen nasa har xuciyarta ta kasa cewa komai sai kallonsa take a sanyaye, Abuturrab ne yyi karfin halin cewa "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un ta rasu Baffa, Bata da lafiya ne?" Alto yace "A'a ko daya, wajen haihuwar 'yar can dai ne Allah ya karba abarsa" ya fadi yana nuna yar yarinyar dake tsaye kusa da Hansai dake matsar kwalla, Tuni Noor ta fara hawaye lkci daya jikinta yyi sanyi sosai, shi kam Abuturrab bai iya ya kara cewa komai ba sai dai tuna irin ynda ta dinga hawaye ranan da xa su bar kauyen yasa jikinsa yin sanyi sosai, bai mance alkawarin da yyi mata na cewa xa su dawo su tafi da ita birni ba, murya Hansai ya katse masa tunaninsa cikin sanyin murya take cewa "Binta ta dde bata yi aure ba bayan tafiyar ku, kullum ba dare ba rana jira take ku dawo ku kai ta birni tayi karatu kamar yanda ta ce kayi mata alkawari, da kyar dangin mahaifinta suka yi mata auren nan, ashe ta ajali ce" ta karashe maganar tana kuka sosai, Alto yace "Ka ji ta kuma...." Cikin kuka tace "To ya kake son in ce Alto" yace "Dama can wa'adin da Allah ya debar mata kenan duniya, kiyi ta mata addu'a don shi kadai take bukata gun ki" Hansai bata kuma cewa komai ba sai share hawayen da ta dinga yi, Kallon yar yarinyar dake gefenta Abuturrab yyi, a hankali yace "Allah ya ji kanta, ya rahama mata, ya kyautata na mu" Alto yace "Amin" Noor kam kasa daina kuka tayi ta rasa dalili, da ta tuna ynda ta dinga kulawa da ita taki sake mata fuska tana basar da ita sai taji duk bata kyauta ba, kukan da take yasa su Arshaq suka fara taya ta su ma, Hansai tace "Hakuri xa mu yi 'yar nn, kiyi shiru don Allah ga shi kin sa 'yan yaran nn kuka su ma, tuni na bar ma Allah komai, Binta ita kadai ya bani kuma ya karbe kayansa ba don bai so na ba, kinga ko dole in ta gode masa, ga 'yar ta nn an maida mata sunan, muna kiranta da Fatima ita na kan gani in ji ddi" Abuturrab yace "Haka ne Baaba addu'ar mu kadai take bukata, Allah ya gafarta mata" Duk suka ce Amin, Abuturrab yace "Amma ina neman wata alfarma gun ku Baffa" Alto yace "To ina sauraren ka Ali, ta me kenan?" Yace "So nake ku koma can cikin Birni da xama don Allah, xan samar maku waje, idan ya so ko wace irin sana'a kke son yi sai in taimaka maka Baffa" Murmushi Alto yyi sosai yace "Allah sarki, ban ki ta taka ba Ali, amma gaskiya ni ko kadan ban sha'awar rayuwar birni na fi son xama a ruga" Hansai tace "Haka ne Ali, ni kai na nafi son nn baxan iya xaman birni ba" Abuturrab yace "Toh shknn, Alfarma ta biyu kuma don Allah baffa kada kace a'a, so nake ka ban Fatima in hada in rike da yarana, ina son ta samu ilimi ynda ya kamata" Hansai ta d'an yo waje da ido, Alto kam murmushi yyi yace "Wani hanxari ba gudu ba Ali, kada ka mance ba mu da iko kan yarinyar nn..." Abuturrab ya katse sa yace "Mahaifinta fa?" Alto yace "Yauwa ynxu kayi magana, bayan rasuwar binta da shekara biyu shi ma ya rasu bayan yyi fama da ciwon daji" Hansai ta tabe baki tace "Dangin sa kuwa duk gantalallu ne, tun bayan rasuwar sa bbu wanda ya tako ganin halin da fatima take ciki, basu san cin ta ba basu san shanta ba, mu kadai ne gatan ta" ta karashe maganar tana matsar kwalla, Abuturrab yace "Toh don Allah ku rabu da su Baffa ku ban yarinyar nn na maku alkawarin xan dinga kawota tana maku hutu, xa ku ji dadin ta nan gaba, kar ku manta muhimmancin ilimin muhammadiyya da boko a xamanin nn da muke ciki" Baffa yyi shiru haka Hansai da ta xuba tagumi, Hansai da wasu sabbin hawayen suka xubo idonta tace "Ita daya nake gani in ji dadi ynxu Ali, idan kuka rabani da ita ya xan yi da raina?" Abuturrab ya sauke ajiyar xuciya yace "Baaba sai ki samu ko d'an 'yan uwa ne ki rike don Allah, ni dai a gaskiya ina son in ma 'yar nn abinda ke ran uwarta har ta bar duniya ku yi hakuri don Allah, sai ma mu iya xuwa da ku ku ga inda muke don lallai duniyar nn ba abun yrda bane tunda ba wai sanin mu ku ka yi sosai ba" Alto yace "A'a ni na yadda da kai Ali, Allah ya shige mana gaba, gata nan ni dai banda abun cewa kuma" ya fadi hakan yana kallon Hansai dake share hawaye tace "Ae shknn, Allah yasa mu dace" Abuturrab yaji dadin hakan yace "Yauwa baaba, in sha Allah xata dinga xuwa maku hutu har ma da yaran gaba daya" Baffa yace "Maa sha Allah, Allah ya taya ku riko" Sai kusan la'asar suka fara shirin barin gidan bayan Abuturrab ya tabbatar su Arshaq sun cinye tuwon tas, amma fa da kyar, Hansae na kwalla ta gama hada ma fatima 'yan tsummokaranta, Dubu talatin Abuturrab ya ba Alto dake ta masa godiya yana sa masa albarka, ita kuma Noor ta ba Hansai dubu goma ta kuma cire layinta dake karamar wayar hannunta ta rubuta masu number Abuturrab a takarda ta mika mata tace "Sai Baffa ya siyo layi a sa a wayar ga Numbersa nan da kun kira xa ku samu" Har bakin mota suka rakosu sai a snn fatima ta fara kuka da Fillanci take tambayar Hansai inda xa a kai ta wanda hakan yasa Hansan kuka sosai, A haka Abuturrab ya ja motar suka bar kofar gidan Noor na daga masu hannu, rarrashin Fatima Noor ta dinga yi da fillanci, Arshaq da kukan ya ishesa yace "Ohh Goodness, Ummu why are we leaving with someone's Child for god's sake? It will look as if we kidnapped her..." Hararansa Abuturrab ya dinga yi ta madubi hakan yasa yayi shiru bai kara cewa komai ba, kafin su shiga kano har tayi bacci, suna isa gida Abuturrab yyi parking ya fito, Noor ma ta fito da little Noor a hannu, su Arshaq suka fito su ma, Abuturrab ya dau fatima dake ta bacci suka shiga cikin gida. *Haske writers asso* 07087865788 for Comment nd corrections!!! You re welcm.