*💫SAKAMAKON ZUNUBI*💫 (THE RESULT OF SIN) ZAHRA ROYAL STAR 08130479973 Dedicated to BOSS BATURE💋 *ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION* FREE PAGE 1-2 Jerin motoci ne suke shara uban gudu kamar zasu tashi sama, duk wasu ababan hawa sun tsaye gefe, an tara uban gosulo a tsakiyar titin. Motocin sunfi guda ashirin daketa wuce wa kamar baza su k'are ba. Wata magana naji daga wata kekenafef, mutanan daya d'akko wata mata, matar ta d'an saki wani tsaki ta ce "fisbilillahi miye hakan anzo an tara mu a nan duk rana na dukan mu akan wani can zai wuce shine za'a wani tsayar da bayin Allah". Mai nafef d'in ne yayi d'an murmushi yana cewa "haba Haj kike wannan maganar baki ga number dake jikin motacin da suke wucewa ba?, baki ga kalar motocin ba ansa *BB No 1* D'and'an Sir Benjamin kenan ba wadda bai san su k'asar nan ba, suna tare da manya-manyan y'an siyasa wadda suke fad'a aji a k'asar nan, saboda tsananin kud'in da suke dashi Mahaifinsa yana da abokai su Uku ne suka had'a wani katafaran Estate tare da gidanjansu kantama-kantama, suka ware kansu daga cikin jama'ar gari, yanzu haka da nake gaya miki wannan wadda ya wuce d'ana ne daga cikin wa'innan mutane, yazo k'asar ne domin shi ba mazauni bane, matukin jirgin sama ne" "Yanzu duk wannan uwar jiniyar da ake mai au bama uban bane d'ansa ne?" "Kware kuwa Haj ai kad'an ma kenan daga, cikin irin kud'in da halalinsa suka mallaka, family d'insu suna d'aya daga cikin masu kud'in duniya. Da yawan mutane sun d'iga ayar tabbaya akan su, domin ba wadda suke so ya rab'e su daga nasu sai nasu" Jinjina kai kawai matar tayi, dai-dai motocin sun gama wucewa, aka bud'e ma sauran ababan hawa hanya. Motocin kuwa har yanzu sun mik'a titi ga mamaki na, sunyi tafiya mai nesa da cikin gari sosai ba kad'an ba. Tukun naga sun d'auke wata hanya data tayi cikin wani k'urk'urumin daji, mai duhun gaske da yalwar bishiyoyi, wata hanya suka mik'a a cikin jejin wadda ta kawo su wani katafaran Estate dai-dai bakin get d'in Estate d'in motocin suka d'an dagata. Idona na zaro d'aga kan da zanyi sai da zuciyata ta buga ganin irin tsaruwar get d'in kansa daga zama an rubuta *BILLIONAIRE'S ESTATE*. Wasu maza masu k'irar sadaukan yak'i sunkai su shadda dake tsoron kafcecen get d'in, sanye suke da bak'ak'en kaya da gilas manne a idonsu tsaye suke k'am ko motsawa basayi. Ganin motocin ne yasa da hanzari suka wangale katon get d'in gidan. Sakin baki da hanci nayi ganin kamar gari ne guda a gaba na. Jerin motocinne suka fara kutsa kansu cikin katafaran Estate d'in. Gaba d'aya kaina ya kwance saboda irin had'uwar estate d'in gidaje ne jere part 6 a ciki, sai k'aton hospital dake ciki ga bishiyoyi masu mugun kyau da suka zagaye ko wanne part dake cikin estate d'in, sai garden Gym area, Swimming pools area, da wurin shak'atawa kai in tak'aice muku harda home beauty saloon, asibitin dake cikin estate d'in na kai idona a kai shima a samansa ansa *BILLIONAIRE'S HOSPITAL* Sai wajan saloon shima ansa *BILLIONAIRE'S SALOON*, Komai daya danganci estate d'in ansa inkiyar gidan a jiki. Tunani na ne ya katse lokacin da jerin motocin da suka tsaitsaya a harabar estate d'in, kusan gaba d'aya mutunan dake estate d'inne suka fiffito domin tarbar Captain Henry daka kalli yadda mutanan gidan suke farin ciki kai kasan ba k'aramin d'an gata bane gaba da baya. Sakin baki na sake yi lokacin da aka bud'e bayan wata mota, sai da aka kai mintina kusan biyar kamin wata k'afa mai d'auke da wani matsiyacin takalmi ta fito daga cikin motor, shi kansa takalmin daka kallesa zaki shaida ba k'ananan kud'i aka kashe ba wajan sayensa, kamin gaba d'aya ya fito daga cikin motor. Alk'alamina ne na kusan yadda sa saboda kyakkyawar halittar Ubangiji da idona yayi tozali da ita. Kyakkyawan matashi ne Captain Henry fari ne tas yadda kasan bature, k'aramin bakinsa yad'an motsa wadda ya d'auke da jan lebe ja jir kamar na jiriri, sai kwayar idonsa ce ta k'arasa rud'ar dani kalar idonsa bulu shar dasu daga tsakiyar su kamar na mage, idan yana kallon mutum kamar mai jin bacci, wadda da yawa y'an mata na sasu cikin wani yanayi. Wani irin miyau na had'e lokacin daya saki wani murmushi na gefen baki, yana bin family d'insa da kallo da sauran y'an uwansa. Kai tsaye wajan wata mata wadda kallo d'aya zakai mata ka shaida mahaifiyarsa ce, ya nufa, yana zuwa ta rungumesa tana shafa kansa tana cewa "Wow my son Henry miss you so much", wani murmushi ya sake sakar mata wadda daga gani kasan ita d'aya ake ma irinsa. Wata matashiyar yariya ce ta taho da gudu tana anbatar sunansa a hankali ya anbaci sunanta itama da cewa "Emily" ya idasa maganar yana rungume ta itama. Murmushi ta saki mai k'ayatarwa tana zuba mai surutu. Bai wani kulata ba gaba, d'aya suka rank'aya sukai wani part wadda ya gaji da had'uwa. "Ai fa Boss ya dawo yanzu zai hanamu shak'atawa wallahi and banso dawowarshi ba. Gashi an kawo wata y'ar aiki zazzafa nake gaya maka ina so na d'anata wallahi" Cewar wani matashin saurayi, ya idasa maganar dai-dai sun zauna akan wasu kujeru dake zagaye da k'aton parlon da suka shiga. Wadda yake ma maganar ya kallesa ya ce "wato Noah da kai da Isaac baza ku daina halin lalata y'an aikin da duk aka kawo estate d'in nan ba kenan ko, sai kun jawo mana wani bala'in ne wai" Wani tsaki Noah yaja yana basarwa ya ce "kaifa Adam kana da matsala wallahi daga gayama abunda ke cikin raina minene a ciki to" "Minene a ciki fa kace duk da ku ba musulmai bane and ko addinin naku bai yarda da irin abunda kuke yi ba, ba addinin daya ce ayi haka, idan kuma k'arya nake ka musalta mana" Sosa k'eya Noah yayi yana tashi hango d'an uwansa yana wani ciccin magani. Isaac ya k'araso wajan yana basu hannu yana cewa "mi ake tattauwana ne kar ayi babu ni" "Uhmm nida wannan Adam d'in mana shima kwata-kwata baya son harkar shak'atawa" Isaac ne ya kai dubansa wajan Adam ya ce "anya Adama kana da ishashshiyar lafiya miye jin dad'in rayuwar to?, idan babu mata a kusa ina bazan iya rayuwa ba mace kusa dani ba" Wani murmushi Adam ya saki yana cewa "shi yasa ma Henry yake birgeni da yake hanaku wasu abun ma yayi dai-dai wallahi, ayi dai mu gani Allah ya shirye ku" Tab'e baki sukai suna amsawa da amin. Dai-dai Henry ya gama shiryawa a part nasa ya sakko, yanzu sanye yake da wata riga har kasa mai k'aramin hannu bak'a ce tayi mai kyau sosai saita k'ara haskaka farar fatarsa, gaba d'aya y'an matan gidan wadda suka gaji da had'uwa da mazan da suke ji da kuruciya da gayu suka zauna akan wani darning mai d'auke kusan mutane goma sha biyar zuwa da ashirin ma, ko wanne ya nutsu yana cin abinci, da yawan y'an matan dake zaune a wajan ko wacce hankalinta naga Henry da Allah yayisa da farin jinin y'an mata ko cikin family y'an matan gidan nasu suna mugun sonsa, ko wacce burinta ace ita ce yake so, dama tunda aka fad'a yau zai sauka k'asar ko wacce ta dage da gyara jikinta. *Takaitattacan Tarihin Billionaire's Family* Hamshaƙan masu kudi wadanda sunan yi yayi sura a fadin duniya, sun shahara A idon duniya, Asalin kafuwar family din mutun ukune tushen shi, wadanda suka kasance aminnan junane, tankar shakikai, amintarsu ta faro tun daga kuruciya har izuwa girman su, kafin samuwar wadatar arxikin su, Almajirai ne marasa galihu muggan takalawa fakirai, jajircewarsu da kwazon su wurin neman nakansu yasa a hankali suka fara kasuwanci wanda daga bisani suka tsunduma a cikin siyasa, Har Allah yakaisu ga matakin da basu ta6a tsammani ba, harta al'umma sun yi mamakin Yadda bayin Allahn nan suka ha66aka a fadin duniya, shin su wanene wadannan Aminnan? Mutun nafarko daga Cikinsu Shine Sir benjamin former president na nigeria, kuma shine mutun mafi wadata arxiki a nahiyar africe, Ya kasance dan kabilan Yoruba ne, sannan mabiyi addinin kristan, yana da mata mai suna Dr Catherine suna kiranta da Mimi. Da yara guda hud'u Capitan Henry shine d'ansa na fari matok'in jirgin sama ne, bai cika zama a Nigeria ba, ya kasance miskili ne na sosai, bai cika shiga harkar daba shafe shi ba, idan kaga yayi magana mai d'an tsawo to tabbas abun nada mahimmanci ne a gare shi, duk cikin familyn billionaire's ana ji dashi, danshi kansa shima ba k'ananan kud'i ya tara ba, sai ko y'an biyu maza Noah, da Isaac, basa jin magana kwata-kwata sune lalata duk wata yarinya da aka kawo aiki a gidan, saboda sunga bata da wani gata gaba da baya. Sun lalata yara da yawa sun maida su kamar matansu. Ga d'an shaye-shaye da suke afawa. Sune yawo can sune can, ga kashe kud'in tsiya kamar mi suna da wulak'anta mutane bare wadda yake k'asansu. Sai kanwarsu Emaily and itama itama dai tana wulak'anci bare ga y'an aiki bata da k'irki ko kod'an, amma duk ciki Henry yafi ji da ita. Sai masu aiki a part nasu akwai Hannah, Amali, Julia, Abigail, sai maza masu goge da share-share, Bayan Sir benjamin mutun nagaba Alhaji Mu'azzam Gidan Dala, Shine mutun na biyu, Ya rike mukamai da dama na yan siyasa, Ya kasance Hausa fulani ne, Yana da tarin arziki naban mamaki Yana da mata biyu ta farko mai suna Haj Saratu wacce suke ma lak'abi da Amma tana da yarinya d'aya mai suna, Ayat sai sai kuma matarsa ta biyu mai suna Haj Shuwa, suna ce mata Ammi, itama tana da yarinya mace Asma, sun kasance suna Matuk'ar son Henry suna kishin junansu akanshi basu cika junatuwa da juna ba saboda ko wacce burinta ace ita ce wacce Henry zai aura, a tsakanin iyayan nasu ma basa wani jutuwa ko wacce burinta ace d'iyarta ce kan gaba ga komai, suna yawan had'ama junansu munafurci saboda ba k'aramin kishi ake bugawa tsakanin Haj Shuwa da Haj Saratu ba. Suna y'an aikin part nasu kowacce nada y'an aiki hud'u biyu maza biyu Mata, Mutun nakarshe daga cikin su ........ Sunan shi Alhaji Habu Anayi mashi lakabi da Barumaye, yana mata mai suna Haj Binta wacce suke kira da Mami tana da yara guda uku na farko Adam, Adam ya kasance yaron kirki ne duk da shima ta wani b'angaran baya da yawan fara'a, amma duk haka idan kuka zauna tare dashi baya son marar son gaskiya duk inda gaskiya take saiya fad'a koda za'a tsire shi ne, sai kuma Aziz shima dai ba daga baya ba wajan rashin jin magana, shima yana shaye-shaye da d'an lab'ewa da yaran masu kud'i y'an mata yana masu b'arin kud'i yana holewarsa dasu. Sai kuma autarsu Mubeena, itama dai akwai d'agawa da nuna ita wata ce, but bata shiga harkar ko wanne part na Estate d'in nasu rayuwarta kawai take, akwaita da son rayuwar k'arya da yawan k'awaye. Tana da k'awaye kusan su uku halinsu kusan d'aya ne da juna Hana Layla da Amira, suma akwai son rayuwar k'arya duk da iyayansu ba wasu hamshak'an masu kud'i bane, shi yasa suka mak'ale ma Mubeena domin tana basu duk wani abo da suke so, shi yasa kullum suna Estate d'in su Mubeena nar su baro cikin gari su taho. Suma suna y'an aiki kusan hud'un, ko wanne d'an aiki yasan part d'in da yake aiki, da kuma irin aikin da yake yi. Duk y'an aikin part d'in su Emaily sunfi shan wahala da kyara, sai kuma y'an aikin su Ayat b'angaransu Haj Shuwa, suma dai suna shan tsangwama, y'an aikin part d'in su Adam ne kawai basa wani shan wulak'anci sai a wajan Maminsa itama ba daga baya ba, bata da son mutane ga nuna d'agawa da nuna ita wata ce. Tasha shiga cikin su Haj Shuwa tana d'agawar ita mai gidanta bai isa yi mata kishiya ba bare har taita b'ab'ato da wata aba wai kishiya. Suna matuk'ar jin haushinta sosai............. *💫SAKAMAKON ZUNUBI*💫 (THE RESULT OF SIN) ZAHRA ROYAL STAR 08130479973 Dedicated to BOSS BATURE💋 *ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION* FREE PAGE 3-4 Henry yana cin abunci kad'an kamar baya son ci, yana ci yana d'an danna wayar dake hannunsa. Wata budurwa dake kusa dashi, ta juya ta d'an tab'o y'ar uwarta dake kusa da ita sosai, d'an kasa tayi da murya ta ce "Asma guy d'in nan fa yayi wallahi dama Abbu zai barni na aure shi ni ba ruwana da wani ba musulmi bane, and tunda Daddynsa duk abokai ne ina ganin kamar bazai k'i ba" Wani murmushi d'ayar ta saki tana cewa a zuci "hmm Ayat kenan idan kinga na barki kin mallaki Henry to bana durun duniya ne, amma babu wacce ya dace ta ita sai ni". Amma a fili sai ta d'an saki wani murmushin yak'e tana cewa "ke kuwa miye zakiyi da Henry kin manta a addininmu ba'a haka, da dai shine musulmi kece wacce ba musulma bane za'a iya hakan". "Amma ta tabbas Asma zan shawo kansa ya musulinta su Abbu ma suna so Daddy Benjamin ya musulinta shida iyalinsa". Tab'e baki Ayat tayi tana harara Asma k'asa-k'asa. Wadda suke ta maganar domin shi ma tuni ya mik'e yana yana hawan bene rik'e da waya manne a kunnansa. K'arar fad'uwar wani abu da suka ji a saman yasa ba shiri suka mik'a su duka, Emily ce ta zaro ido tana nufar kan benan inda Henry yake rik'e da wata matashiyar yarinya wacce bazata wuce shekara goma sha takwas ko sha tara, da ka kalle ta zaka shaida y'ar aiki ce domin sanye take da wani yadi kalar sararin samaniya yinifom, riga da wando rigar ta kai mata har gwaiwarta, ganshin kanta ya rufe mata fuska. Zero ido tayi cikin tulin gashin daya rufe mata fuska, ba abunda k'irjinta yake sai lugudan bugawa, na tsananin tsoro, domin kawai tana sakkowa ne kanta a kasa tana son barin parlon kamin wani ya lura da ita. Domin tasan halin gidan gaba d'ayansu basu cika mutumci ba, duk wani wadda yake aiki a k'ark'ashinsu su wulak'antaka ba wani abu bane a wajansu, na kirkin y'an kad'an ne daga cikin su. Tunanin ta ne ya katse jin an fisgota daga jikinsa sai dai taji saukar mari tasss tassss kake ji k'arar marin ta karad'e gaba d'aya babban parlon. Saukar maganar Emily taji a kanta da masifa tana cewa "ke Amalil Islma wacece ke? har kin isa had'a jiki da brother na kina y'ar aiki dake k'ask'antacciya dake k'azama, to kin jama kanki mummunan horo a waje na, shashasha bagida jiya kawai". Wasu irin hawaye ne suka shiga zuboma Amalil dake tsaye tana duban yadda Emily take surfa mata ruwan rashin mutumci, tana da tabbacin ta girmeta amma talauci da rashin galihu yasa tana wulak'antaka, yaya zatayi dole ne zama a k'ark'ashin su tunda tunda ta taso a gidan kawai ta ganta, wasu daga cikin y'an aikin suna yawan bata labarin Mahaifiyarta ai wajan haihuwarta ne ta rasu kuma ta barta a gidan, ta d'ora da bautar da Mahaifiyarta tayi can baya. Da sauri taja himar d'in dake sanye a wunta ta gyara gashinta daya fito tana had'e wani abu a zuciyarta. Hakuri ta cigaba da bata amma yadda kasan ana zuga Emily yadda take ruwan masifa, shi ko wadda ake abun danshi tuni yabar wajan. Bak'in ciki duk ya cika Amali data bisa da kallo kenan ma mazai tsawatarma k'anwarsa ba?, duk tasan halinsa ko mi za'ai indai bai shafesa dole ba baya ma sa baki bare har ya shiga harkarka miskili ne na bugawa a jarida. Marin da aka k'ara kaima Amali ne ya dawo ta ita daga bin Henry da kallo da tayi. Bin Asma tayi da kallo data mareta ta cakumo mata wuyan riga tana janta kiiiii tana nufar waje da ita tana cewa "kee mayiya uban mi kike kallo a jikinsa?, au dama kina sane kika fad'a jikin nasa kenan?, kega karuwa y'ar iska, to ki bud'e kunnanki kiji da kyau kinsan suwaye mu kinsan Henry yafi k'arfin ki nesa ba kusa ba, bakin rijiya ba wajan wasa makoho bane, ki kiyaye koda kallonsa ne idan ba haka ba, na rantse saina yi sanadiyar nakasa idon naki" Shuru wajan ya sake d'auka, Adam na so yayi magana amma Maminsa tayi mai mugun gargad'i da ido, sauran samarin gidan kuwa ko a jikinsu saima komawa sukai suka ci gaba da cin abincin su hankali kwance. Banko k'ofar parlon da akaice yasa Amali sakin kukan dake taso mata tun d'azo, tana kuka ta nufi part d'in y'an aikin gaba d'aya estate d'in da yake waje guda aka ware masu. Duk da kowanne d'an aiki da gidan da yake aiki na cikin estate d'in guda shadda dake cikin estate d'in. Koda ta shiga b'angaran nasu babu kowa duk sun tafi inda suke aiki, shiga d'akinsu tayi wadda yake d'auke da jerin gadaje kusan guda goma, saboda k'aton d'aki ne, babu abunda ba'a sa musu ba harda fankar sama data k'asa sai toilet guda uku dake a cikin d'akin duk da d'akin bashi kad'ai bane akwai kusan guda biyar dake jere da juna kuma ko wanne d'aki na d'auke da gajen guda goma da toilet uku a cikinsu, part mata daban na maza ma daban, duk yawan su ko wanne da irin aikin da zakiji yana yi wani wanki da goga wani wanke-wanke wani girkin abinci, wani goge-goge, wani ma gogar takami ne kawai aikinsa, kai kowa dai da abunda yake yi. Ita Amali tana d'aya daga cikin wadda suke aiki shashinsu Emaily, kuma abinci take girkawa, suna shan wahala sosai dan a rana sai suyi abinci ya kai kala goma koma fin haka, mutunan gidan suna ji da milki da isa suna gadara da kud'i. A can parlon su kuwa Emily dake kallon Asma tana murmushi ta ce "hey sister kinyi dai-dai wallahi, ai ki barni da ita, saina gyara mata zama ne, shegiya kodan ta ganta da kyau?" Wani yatsine baki Asma tayi tana amsa da cewa "har wani kyau ne da ita ni banga kyan ba gaskiya mi take dashi?" Duk abunda suke Ayat na kallo tana sak'a wani abu a ranta, wani murmushi ta saki tana tono yadda zatai rink'a anfani da Amali tana k'unsa ma Asma bak'in ciki akan Henry, tabbas zatai anfani da ita, kodan ta jefi tsuntsu biyu da dutse d'aya, zata sa a k'ara tsanar Amalin, sai kuma Asma da zata rink'a kwasar bak'in ciki............. *💫SAKAMAKON ZUNUBI*💫 (THE RESULT OF SIN) ZAHRA ROYAL STAR 08130479973 Dedicated to BOSS BATURE💋 *ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION* FREE PAGE 5-6 Tab'a tan da akai ne yasa da sauri ta tashi tana share hawayenta matsowa kusa da ita Hannah tayi tana sa hannunta ta dafa kafad'arta, cike da tausayin su ta ce "Amali lafiya dai na ganki a haka, ko dai mutanan gidan nan ne suka yi miki abunda suka saba yi ne?". Wani murmushin k'arfin hali Amali tayi tana duba agogo, da sauri ta mik'e tana cewa "karka damu Hannah bari na je wajan Emily tana jira na, kinsan lokaci take badawa idan banje akan time komi zata iya min" "Ai nima bari mu tafi tare zanyi mata wankin kaya" Da sauri suka fice suna jawo k'ofar d'akin nasu. Suna shiga kai tsaye part nata suka nufa, koda suka shiga tana waya ne da wani saurayinta, samun waje k'asa sukai suka zauna suna faman jiranta tana waya tana kurb'ar shayi. Sai da ta d'au kusan minti 40 tana waya tukun ta aje wayar a nan ma sai da ta nuna kamar ba mutane bane a gabanta, sai da ta mula ta munl-mule. Ta d'ago tana binso da hararara. Suko dama duk zaman ya gunduresu babu yadda zasuyi ne. Wani tsaki ta saki mtswwww tana ya tsine baki, a tsawace ta ce "ubanmi zanyi muku?, kuka wani zo kuka zaunawa mutane a nan, sai wani wari kuke kun cika min d'aki da wari". Da sauri Amali tayi k'asa da kanta tana duba jikinta harda d'an shinshina jikinta koda wai zataji warin da aka ce suna yi, amma itakam bata ji wani wari ba. Tsawa ta kuma buga masu ta ce "keee Amali dubanni nan". Da sauri Amali ta d'ago tana kallon Emily, sai dai d'ago war da zatai taji saukar ruwan shayin dake hannun Emily ta watsa mata shi a fuska. Runtse idonta tayi tana jin wani rad'ad'i na ratsa mata fuska. Wasu hawaye ne suka shiga zarya akan fuskar tata. Hannah dake kusa kuwa da sauri ta zaro ido, tana sa tafin hannunta ta tushe bakinta. Kallonta Emily tayi tana cewa "kee Hannah tashi ki bar wajan nan munafaka, kin wani zauna min a nan baki san aikinki bane?". "Amma ranki ya dad'e ke ce kika ce idan na zo na rink'a tsayawa harsai kin ban umarnin farawa tukun sabo.... Katseta tayi a tsawace ta ce "dalla can rufe min bakinkin nan mai wari, munafuka kawai bagidaji zaki tashi kibar wajan nan ko sai na zamga miki mari?". Da sauri Hannah ta mik'e har tana tuntub'i tayi wajan b'an d'aki domin yin aikinta, jikinta duk a sanyaye tana waigen Amali dake zaune kanta a k'asa. Emily ta dawo dubanta ga Amali ta ce "kee kuma yau ina so ke kad'ai zakiyi min abincin mutum ashirin da biyar, idan kin gama ki gyara Babban parlon gidan nan, zaki iya tashi kiban waje". Wata irin zabura da zare ido Amali tayi ta ce "ranki wannan aikin banzan iya yinsa ba ni kad'ai, ki tausaya min dan Allah". "Ke rufe min baki zaki tashi kibar wajan nan ko saina miki shegen duka, kuma nanda minti goma idan na sakko baki fara aikin dana saki ba to tabbas horon da zan miki sai ya fi wadda nayi miki yanzu, dalla tashi kiba mutane waje". Emily ta idasa maganar tana bin Amali da wani banzan kallo na k'as-k'anci. Da sauri Amali ta tashi jikinta a sanyaye tayi waje. Koda ta shiga k'aton kitchen d'in part d'in nasu Emily, tsabar girma da da fad'i kamar wani d'aki guda, bin kitchen d'in tayi da kallo kamar ganin babu kowa kenan duk an kori kowa ana nufin yau ita d'aya zatai duk wani aiki daya shafi abinci. Da sauri ta fara aikin, tun tana yi da marmari, tana yi ta sauke wannan ta d'ora wancan, kanta harya fara juyawa tsabar yadda ta jigatu tasha bak'ar azaba kamin ta gama abinciccikan nan. Wani irin jiri take ji da kyar ta lallab'a ta fara gyaran k'aton parlon da kai girman wani gidan. Tana idasa kyaran ta zube, wajan a sume saboda wani irin bala'in jiri dake d'ibarta ga yinwa bata ci komai ba. Emily dake sakkowa taci uban wanka an zubo gashin doki har gadon baya, ansha k'ananun kaya ana cin chingum ana taku d'ai-d'ai. Jan birki tayi tana duban Amali dake yashe a k'asa, duk taga kamar ba k'alau take ba amma hakan baisa ta tausaya mata ba, da wata irin tsana ta nufi firiza tana d'akko ruwa mai sanyi tana zuwa kan Amali ta b'alle murfin ruwan ta fara kwarara mata shi a jiki. Wata irin zabura tayi har lumfashinta na shid'ewa tsabar yadda ruwan sanyin ya shigeta. Da sauri ta mik'e da kyar ta tsaya kan k'afafunta saboda kwata-kwata bata da k'arfi a jikinta. Emily tayi mata wani d'an iskan kallo tana cewa "uban mi kike a nan?". Amali ta had'e wani abu mai d'aci a mak'oshinta ta ce "ranki ya dad'e babu komai banma san na fad'i a wajan ba", "yen yen yen da anyi magana kin iya munafurci da iya zaro zance kega tsohowar munafuka, and kin gama aikin dana saki ko kuwa?" Da sauri Amali ta ta bata amsar ta gaba d'aya, amsar data bata ce ta bata haushi ta ce ma Amali "kin taimaki kanki and zakiyi kwana uku kina min abincin nan fatan kin gane?" Wasu hawaye ne suka cika idon Amali tana amsawa a ladabce. Tana tsaye saida tayi kusan minti biyar tukun Emily ta bata umarnin zata iya tafiya. ISAAC AND NOAH POV Zaune suke a wani lanbo dake cikin estate d'in nasu suna shan lemo, Julia ce take ta sintirin kawo masu kayan ciye-ciye, tana yi tana gyara suturar dake jikinta domin ta lura da wani d'an iskan kallo da suke binta dashi. Allah-Allah kawai take ta gama aikinsu ta tafi, karda suyi mata wani mugun abun. Sai dai tana gaf wucewa har tana murnar ta gama basu mata wata maganar banza ba. Kawai taji muryar Isaac yana cewa "kee Julia kike ko kowa dawo nan". Wani irin miyau Julia ta had'iye , ta juya ta nufi inda suke zaune ta duk'a k'asa, kanta a k'asa zuciyarta na wata irin bugawa tsabar tsoron daya dirar mata. Batai aune ba kawai taji Isaac ta jawota, sai ganinta tayi zaune akan cinyarsa yana k'ok'arin sa hannunsa a cikin rigarta. Da sauri ta rik'e hannunsa tana girgiza mai kai hawaye nabi mata fuska, kallonta yayi da haushi ya fisge hannun nasa yana kifa mata wani mari mai zafin daya sa ba shiri ta sakar mai hannun nasa. Bai tsaya komai ba yasa hannunsa biyu yana kamo gaban rigar Julia yajata da mugun k'arfi ji kake feeeet ta yage gida biyu. Wani irin marayan kuka ta saki tana sa hannunta domin k'are k'irjinta, sai dai Noah daya taso ya rik'e hannun nata ya jasa baya ya bank'are mata hannu ya jasa baya har sai da ya bada wani sauti k'as. Wani kuka ta sake saki. Wani kyalli Isaac ya d'akko ya d'aure mata baki dashi, sana Noah ya sureta yayi part d'insu da ita Isaac na biye dashi. Koda suka shiga a tsakar parlon su suka ajeta suka cire kaya a gabanta su duka sai da sukayi anfani da ita, harda inda ya kusan sa zuciyarta bugawa, saboda harta duburarta saida sukayi anfani da ita, bak'in ciki ya cika mata zuciya kukan ma ta kasa sai sauke ajiyar zuciya take. Suna gamawa Noah ya tashi yana tufa mata miyau a fuska. Da sauri ta runtse idonta hawayen bak'in ciki da tsananin tsanar su na zubo mata ta gefen idon ta. Tsawar da suka buga mata ce yasa da kyar ta mik'e. Wurgo mata kayanta da suka keta su, sukayi masu fata-fata. Isaac ya ce "dallah tashi daga nan, kuma ki tabbatar kin kyara mana parlo ki tabbatar kin kyara wannan k'azantar". Binsu kawai Julia tayi da kallo har suka haye sama, da kyar ta samu da d'angyanshi da rarrafe ta d'an gyara parlon, tasa kayanta ta nufi k'ofar fita idonta jawur da kyar take tafiya k'afafuwa duk a gwale.......... *💫SAKAMAKON ZUNUBI*💫 (THE RESULT OF SIN) ZAHRA ROYAL STAR 08130479973 Dedicated to BOSS BATURE💋 *ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION* FREE PAGE 7-8 "Adam wato ba zaka daina shiga harkar da babu ruwanka ba ko?" "Amma Mami kina ganin irin cin fuskar da suke ma wannan yarinyar Amali kuma ace ba wadda yayi magana" Kallon sa Mami tayi tana k'ara cewa "to ina ruwanka a ciki?, miye matsalarka da ita?, hakan ai shine ya dace da talaka tunda dama bauta ce ta kawota dole kuma tayi hakuri tunda a k'ark'ashin wani take, kaga kuwa dole a juyata". Zai sake magana ta d'aga mai hannu ta sake magana ta ce "kaga dakata Adam daga yau duk abunda zai faru bana so kana tsuma bakinka, indai abu bai shafeka ba". Ba yadda ya iya kawai ya fice daga part d'in nasu yana jin wani iri a ransa. Yana fita Mubeena tayi sallama tare da k'awayenta su uku suna tafe suna rufa mata baya Mami ce tayi murmushin ganinsu, Mubeena ta d'an tsaya tana kallon Mami ta ce "Mami yana ganki haka?" "Uhmm" sauke lumfashi Mami tayi tana jawo hannun Mubeena ta zaunar da ita ta ce "nida Yayanki ne mana ya cika shiga abunda babu ruwansa a ciki" Tab'e baki Mubeena tayi tana mik'ewa ta ce "ai Mami indai Ya Adam ne ya saba da hakan dan haka ki daina ma damun kanki, amma nidai kam dama kowa ya sani bana shika shirgin family d'in Estate d'in nan tamu kowa yayi harkarsa, sai idan kaine ka shiga tawa harkar nanne fa za'a sha kallo danni kinsan Mami bana son raini a rayuwata" "Ai Mubeena ke ni ce kika biyo duk wasu halayanki amma banda Adam sai kace an canza min shi wallahi" Kiss kawai Mubeena ta kai mata ta juya ita da k'awayenta da suka gaida Mami ta amsa fuska a sake, suka fara haurawa sama Mubeena na tafiya tana cewa "Mami wai yaushe su Abbiey zasu dawo ne sunfa dad'e?" "Eh kinsan dama idan suka tafi harkar kasowancinsu da harkar siyasar nan sai a hankali amma cikin satin nan zasu dawo shima naji Sir Benjamin sai tafi k'asar India cikin satin nan" Da sauri Mubeena ta waigo inda Mami take ta ce "shin wai shi Daddyn su Henry ba zai hakura da siyasa ba wannan zab'enma sai ya ce saiya tsaya takara, da alama neman asiri zaije India dan kinsan ba wadda ya kaisu iya asiri da sihiri wallahi" "Kinci gidanku ina ruwanki idan basa irin haka an gaya miki zasuci zab'en ne ki wuce kawai ku shiga ciki, wannan zancen ba naku bane" Shuru Mubeena tayi tana d'an d'aga kafad'arta irin ko a jikinta d'in nan. Ayat dake zaune akan kujerun parlon su tana kallon wani film, taji Amma ta tab'a ta tana cewa "da alama ba kallon nan kike ba, domin tun d'azo nake ta miki magana amma baki ji ba hankalinki na wani waje, mi yake damunki ne?" "Tabbas Amma akwai matsala ina son Captain Henry amma Asma tana shigarmin hanci da k'udundine wallahi" "To kina buk'atar fiddota kenan?" "Tabbas Amma haka ne, ina so na shirya mata wani tugun da zata rink'a kwasar takaici" Murmushi Amma ta saki tana k'ara dafa k'afadar Ayat ta ce "karki damu mudun ina lumfashi Asma ita da uwarta bazasu tab'a mallakar wani abu mai daraja ba, ke dai kawai ki cigaba da k'ulla masu munafurci ni kuma zanje ga boka na d'an mukyakis zai min wani aiki akansu" Wani tsalle Ayat ta saki tana rungume Amma tana cewa "shi yasa a bana jinki Amma, Amali zan had'ama tarko domin itama na tsani yarinyar da ace nan part d'inmu take aiki da tuni nasa an koreta daga estate d'in nan, domin idan kika lura yarinyar nada wata baiwar kyau mai fisgar mutum, tare da wata baiwa duk namijin da yayi katari da ita dole sai ya kalleta ya sake kallo, wai a haka ma cikin wahala take inaga ta samu waje, ai ba'a san yadda zata koma ba" "Kashhh wannan ma ki daina tunaninta, domin bazata bamu matsala ba, idan kuma zata bamu ai baza tai wahalar kawar da ita bama a duniyar gaba d'aya, wa take da shi?, waye gatanta a duniya?, waye ubanta? bata da kowa bare har ta d'au kanta wani abu baiwace kuma y'ar aiki kuma a haka zata cigaba da zama". Murmushi kawai Ayat take saki tana sauraran Amma. Tashi kawai Ayat tayi ta d'au wani k'aramin mayafi tana nufar k'ofar fita daga part d'in, da sauri Amma ta ce "ina zuwa kuma Ayat muna magana kawai zaki tashi?" "Karki damu Amma yanzu zan dawo kinsan da zafi-zafi ake bugun k'arfe ina zuwa". Tana idasa fad'ar haka tayi waje. Fitowarta kuwa ta hangi Amali dake fitowa daga part d'in su Emily, wani murmushi cin nasara tayi tana kwalama Amali kira. Amali dake tafiya a hankali saboda aikin da Emily ta sata da kyar take tafiya, tana k'araso, ta ce "ga ni ranki ya dad'e" Wani banzan kallo Ayat ra wurgama Amali kamin ta ce "ina kiranki kina min wata yanga, ubanwa zakiyi ma yanga a nan wajan iyeee?". Wani abu mai d'aci Amali ta had'iye a mak'oshinta cike da takaicin mutunan gidan gaba d'ayansu ta ce "kiyi hakuri bana jin dad'i ne". Tab'e baki Ayata tayi tana cewa "ki biyo ni". Tana fad'ar haka ta juya tayi cikin part d'in. Bin bayanta Amali tayi, har suka shiga cikin parlon gidan basu tsaya parlon Amali taga sun nufi kitchen, tana zuwa taga Ayat ta d'akko wani lemo da wasu kayan ciye-ciye tasa a faranti tana mik'ama Amali ta ce "ungo nan kije part d'in Henry ki kai mai" Zaro ido Amali tayi tana kallon Ayat ta kasa amsar farantin, wani banzan kallo ta bita dashi tan cewa "kee ni sa'arki ce zance kiyi kaza, ki tsaya kina bina da kallo, zaki amsa ki wuce kije ko kuwa sai na ci miki uwa?". Wani irin abu taji ya rik'e mata k'irji dan taji zagin da Ayat d'in tayi mata ta tsani a zagar mata iyaye, cike da jin haushin Ayat d'in ta amshi farantin bata k'ara cewa komai. Ta juya zata tafi taji muryar Ayat na cewa "saura kuma idan kika je baki gansa ba ki juyo ki taho baki basa ba, ki tabbatar ya ganki ya amsa da kansa, kinji na gaya miki?" Wasu hawaye ne Amali taji sun tarar mata a cikin ido, da sauri kuma ta mayar dasu, bata dai ce komai ba ta fice kawai. Tana fita daga part d'in ta tsaya cak tana duban masu tsaro kota ina a cikin estate d'in sai shawagi suke bare a k'ofar part d'in Sir Benjamin, shine yafi kowane part girma a gidan, da tsoro da komai ma, duk da yana d'an siyasa bai zauna gidan gwammanati ba, yafi son zama a cikin estate d'in, tana tunani tasan idan ba tana y'ar aikin gidan ba ita ai bata isa koda taka inda d'an president yake ba bare harta sa president d'in a idonta tasan komai sanadi ne, ji yadda ake basa tsaro shida y'ay'ansa kai duk wadda ke cikin estate d'in ma idan zai fita cikin gari haka zakaga ana mai jiniya tare da motoci nabin bayansa. Tana tunani harta k'arasa inda part d'in Henry yake, duk haka sai da masu tsaron part d'in suka dakatar da ita suka duba abunda ta d'akko tare da dubata ko ta taho da abun cutarwa, duk sunsanta sun san ma'aikaciyar gidance, amma haka k'a'idar take, idan shiga goma zakai sai an cajeka. Koda ta shiga k'aton parlon, wani k'amshi yayi mata d'irar mikiya daya sa sai da ta lumshi idonta tsabar yadda k'amshin turaran ke shiga ta k'ofar hancinta. Sauke ajiyar zuciya tayi, tana tsaye ta rasa inda zata nufa da kayan dake hannunta. Gargad'in da Ayat tayi mata, ba yadda ta iya ta haura sama inda take d'anjin motsi. Koda ta shiga yana zaune ya d'ora k'afa d'aya kan d'aya, yana aiki a computer sai wani mutum dake tsaye gefensa yana masa bayanin wasu takardu yana nuna mai. Jin shigowar mutum da sallama yasa mutunan dakatawa da yimai bananin, tunda ya kalleta sau d'aya ya maida dubansa ga computer, sai mutunan data ji ya kira da suna Osman, ne ya kalle ta yana cewa "ranka ya dad'e kaine kasa a kawo ma abinci ne?". Sai da aka d'au minti talatin kamin yad'an motsa bakinsa kamar baya son magana ya ce "No, I don't know about him, to be honest", Shine kawai ya ce ya tsuke bakinsa, wani haushi ne ya cika Amali jin yadda ya amsa, to ita ina ruwanta dashi cewa akai ta kawo mai kawai. Osman ya ce "zaki iya ajewa ki tafi" Da sauri Henry ya dakatar da ita, shuru sukai Amali ta cigaba da tsayuwa su kuma suka cigaba da aikinsu. Amali tun tana tsayuwa da marmari harta gaji ta rasa ta inda zata fara magana ma. Har sai da Osman ya gama mai bayanin komai ya sallameshi ya tafi Amali na tsaye kamar wata g'unki, bak'in ciki ya gama cikata sai harararsa take tana murgud'a mai d'an k'aramin bakinta. Duk yana kallonta ta k'asan ido wani miskilin murmushi ya saki yana dubanta maganarsa bata fita sosai saboda jin kai ya ce "Who brought me food and it's not your job?" Sai da ta murgud'a baki sana ta ce "ni nasa kaina" Baiji mi ta ce sosai ba saboda itama kamar rad'a maganar ta fito, kallonta yayi na wasu y'an mintina tukun ya ce "am taking to you" Sauke ajiyar zuciya tayi ta sake cewa "ni ce nasa kaina" "Who told you that I need food?" Wani haushi ne ya kamata bata k'ara magana ba, shima shuru yayi, ya k'ara barinta a tsaye har saida Amali tayi danasanin fad'ar haka, yafi hawa d'aya yana aiki a computer kamar wani injin ko gajiya baya yi. Tukun yayi mata nuni da hannu ta aje kayan. Tana ajewa zata juyawa ta tafi taji muryarsa yana cewa "I told you to go?" Wani irin takaici ne ya rufe Amali, har bata san sadda ta fara bubbuga k'afa ba tana tab'e baki alamar tana gaf sakin kuka. Shi ko kallonta take ta k'asan ido yadda tayi kamar zata mai shagwab'a shi dariya ma ta bashi, amma ya maze, idan ka kallesa saika rantse da Allah ba ita yake duba ba. Ci gaba yayi da safgar gabansa, sai da Amali ta k'ara kusan mint ashirin harta fara hawaye, tukun taji saukar muryarsa mai kamar busar sarewa ya ce "You can go, from today you can do the work that has not been released" Harara ta b'alla mai ta juya ta tafi, tana masifa a zuciyarta, au duk tsayuwar da tayi dama babu abunda zatai mai tsabar mugunta ce dama gashi ba wani jin dad'i take ba, ai ko kyar take taka k'afarta saboda yadda sukai mata nauyi saboda yadda tasha tsayuwa.......... *💫SAKAMAKON ZUNUBI*💫 (THE RESULT OF SIN) ZAHRA ROYAL STAR 08130479973 Dedicated to BOSS BATURE💋 *ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION* END OF FREE PAGE 9-10 Fitowar da Amali zatai kawai taji an d'auketa da wani gigitaccan mari tassssss tassssss. A gigice Amali ta dafe kumatunta, da masifar sauri ta d'ago tana duban wacce ta mare ta. Ba kowa ba ce face Asma, tun d'azo ta hangi Amalin dake fitowa daga part d'in Henry, wani irin kishi ya ciyota har bata san sadda ta k'araso inda Amalin take ba, dan ita a tunaninta sonshi take tana shishshige mai dan har idonta ke mata gizo da Amalin tana fitowa tare da wani murmushi a fuskarta. Kamin zafin marin ya saki Amali ta k'ara jin saukar wani a tsakiyar idonta, runtse idonta tayi da mugun sauri lokaci d'aya jini ya kwanta ta jikin idon, tama kasa magana sai bin Asma take da wani kallon takaici. Can ta tsinkayi muryarta cike da tsananin masifa tana cewa "wato kwartonci kesa kina shishshige ma Captain Henry ko?, saboda y'ar iska ce ke dama mai bin mazan mutane, to ki bud'e kunnanki da kyau kiji ni, wallahi tallahi na k'ara ganin kina shishshige ma Henry wallahi zan iya halakaki indai a kansa ne, ke kowa ma zan iya kawarwa mudun zai bani matsala akan na mallaki Henry, ke kuma k'aramar alhaki bazaki min wahalar b'atarwa ba, dan haka tun wuri kima kawar da maitarki akan Henry, domin Henry na Asma ne ni kad'ai, dan haka ki kiyaye ni ki fita ido na rufe tunkan nasa a b'atar dake a doron duniyar nan gaba d'aya, kinsan waye uba kin san abunda na fad'a mai sauk'i ne, baki da kowa, ke idan baccin k'arfin hali dake gare ki ina ke ina d'and'an president, ai kaurin idonki ma ya isa Amali, nidai gargad'i nayi miki idan kunne yaji gangar jiki ta tsira". Tana idasa fad'ar haka tayi wucewarta tabar Amali tsaye tana tsiyayar da hawaye. Part nasu na masu aiki ta nufa tana tafiya tana kukan zuci da hawaye dake anbaliya a fuskarta. Tana gaf shiga d'akinsu taji kukan Julia da Hannah, suna shashshakar kuka. Da hanzari ta fad'a d'akin tana faman tabbayarsu mike faruwa?. Da sauri Hannah ta rungume Amali tana cewa "Amali tsoron gidan nan ya cika min zuciya kina gani fa daga kawo Julia baifi sati d'aya ba, amma yau wa'incan na mamajon Isaac da d'an uwansa suka farmata suka lalata mata rayuwa, Amali sun tarwatsa mata rayuwa, ina gudun wata rana nima abun nan yazo kaina anya bazan gudu daga estate d'in nan ba". Wata irin fad'uwar gaba ce ta riski Amali da sauri ta runtse idonta wasu sabbin hawaye suka sake wanke mata fuska, kallon Julia take da duk tasha kuka ga fuskarta data kunbura da shatin mari a fuskar tata, kai hatta jikinta duk ciwo ne domin fara ce Julia. Amali tana kallonta bata san sadda ta k'ara fashewa da kuka ba, tana shanye duk wani abu na yau da akai mata, tana fuskantar Julia. Tama rasa da wata kalma zata fara rarrashinta, tabbas ko wacce kalma da zatayi anfani wajan bata hakuri tayi kad'an tabbas an cuceta an gama da ita. Da kyar ta samu bakinta ya furta sunan Julia tana cewa "Julia na rasa ma ta ina zan fara baki hakuri, Julia tabbas an cuceki amma ki sani idan ba nan akwai can, wadda Allah da kanshi zaiyi maku hisabi keda so, kiyi hakuri kawai ki mik'a kukanki wajan Ubangajin da baya bacci kiyi hakuri kiyi hakuri kawai, amma tabbas mutunan gidan nan gaba d'ayansu basu da imani ko musuk'ala zarratin". Julia na kuka, da gurb'atacciyar hausarta ta ce "tabbas Allah zai saka min, Allah ya saukarma da mutunan nan bala'in da bazasu iya maganinsa ba, Allah ya nuna masu ba komai kud'i ke maganinsa ba", ta k'are maganar tare da gunjin kuka. Hannah ce ta sauke lumfashi tana cewa "tabbas duk da ke ba masulma ba ce amma Allah na kowa ne tabbas Allah zaiji kukanki kuma zai kawo maki d'auki dama mu duka gaba d'aya domin ana shiga hak'k'inmu". Da kyar suka taimaka Julia ta gyara jikinta tanayi tana kuka tsabar yadda gabanta ke mata zugi abunka da ba'a sababa, ba k'aramar illa sukai mata ba, dandanan zazzab'i ya rufe ta. Su Amali suna tare da ita suna bata kulawa. Har sadda sauran ma'aikatan gidan suka dawo, sai tabbayarsu suke ko lafiya. Inda basu sanar ainahin abunda ya faru ba, saboda wasu koda ka fad'a k'aryata ake koda mutum ya sani, kai koda abun ya tab'a faruwa dashi shima, amma yadda kasan asiri ake masu haka suke ji basa iya d'aukar ko wane irin mataki bare har suyi magana akai, to idanma sunyi magana masu kasar ne fa gaba d'aya miye doka zatayi masu suda sune dokar gaba d'aya, dama ance wata shari'ar sai dai a lahira. *K'ASAR INDIA* Zaune Sir Benjamin yake a gaban wani k'aton mutum mai sanye da wasu layu da jajayen kaya a jikinsa, wata irin dariya yake b'ab'b'akawa wacce tsabar dariyar da yake tasa d'akin da suke zaune fara gigizawa kamar kasar wajan zata tsage gida biyu. Wata murya dake fitowa daga bakin bokan kamar saukar aradu mai cike da wani irin amo marar dad'in sauraro. Yana cewa "tabbas tunda kazo nan da buk'atarka ta gaba biyu zaka koma akan kujerar milkinka, amma sai kayi wani aiki mai hatsarin gaske idan kaga zaka iya to ba shakka gaka can kaci zab'e. Sir Benjamin dake zaune ba alamar tsoro ko damuwa ya ce "tabbas boka ko miye zan iya yi tunda kaga na d'akko k'afa yau tun daga Nigeria zuwa nan ai kasan babu abunda bazan iya yi ba, kawai a fad'a min miye zanyi boka". Wata dariya bokan ya sake kecewa da ita yana cewa "zaka samu y'an mata guda biyu y'an shila wadda ba'a tab'a kusantarsu ba, zakayi anfani dasu amma harda ta duburarsu, wannan ruwan maniyar da zaka zubar wajan saduwa dasu zaka ajiye jan a wajan da kake saduwa dasu. Ana so maniyin ya zuba a jan kyallen, sana kana gamawa dasu kayi masu yankan rago jinin da zai zuba a jikinsu zamu aiko da aljani zai tsutse sa, daga nan zai d'au jan kyallen da ka tara maniyinka dana y'an matan, abu na gaba za'a samu jarirai sabowar haihuwa aljani zai sha jininsu". Koda gama wannan bayanin sab'anin Sir Benjamin yaji tsoro ko ya ce bazai iya ba, sai ma wani mugun murmushi ke fita ta fuskarsa, ya ce "shine kad'ai abunda za'a aiwatar boka". Wata shegiyar dariya boka ya saki yana cewa "tabbas irinku muke so wadda basa da tsoro ko shakka wajan cikar burinsu, tabbas idan ka aiwatar da komai yadda na fad'a maka zakayi mulki yadda kake so" Shima Sir Benjamin dariyar ya saki yana cewa "dana koma duk za'a aiwatar da abunda kasa". "Idan kuwa kayi haka kaima zaka ga sakamako ranar zab'e. Koda Sir Benjamin ya fito kai tsaye mota ya shiga sauran jami'an dake tsoronsa suka rufa mai baya kai tsaye filin jirgi suka nufa, koda suka isa jirgi shi kad'ai yake jira domin shi kad'ai da jami'an tsaronsa zai d'auka. Basu wani b'ata lokaci ba suka tashi, sai da sukayi kwana d'aya da yini sana suka iso Nigeria. Wasu matsitan motaci ne suka zo tarbarsa kusan guda ashirin bak'ak'e ne masu mugun kyau tare da jami'an tsaro kota ina. Yana hawa mota suka fara tafiya akan titi duk inda suka gifta sai ansan wani ne a k'asar ya wuce. Sir Benjamin suna cikin mota ya kalli P'A d'insa, wadda duk wani abu da suke shiryawa ta rashin gaskiya ya sani tare suke yinshi shi yake samo komai. Ya ce "ina so a samo min y'an mata guda biyu akai min su gidan hutawa ta, sana abu na gaba ina so a samu min jarirai d'anyar haihuwa". Gyara zama P'A yayi ya ce "ranka ya dad'e samo y'an mata bazai wahala ba domin yawancin y'an matan yanzu son kud'i gare su, dan ayi masu wayau a halaka su ta sanadiyar kud'i ba wani abu bane mai wahala. Kawai dai samo jariran ne kamar zaiyi wahala". Wani murmushi Sir Benjamin yayi yana latsa wayarshi ya ce "idan komai ya tafi dai-dai da mutanan da kukayi aikin dasu kowa zai iya samun million goma-goma". Zaro ido P'A yayi yana had'e wani miyau yana mai-maita million goma. "Kware million goma", cewar Sir Benjamin. Har jikin P'A na kyarma wajan cewa "ai ranka ya dad'e kasama ranka anyi an gama, zuwa gobe duk za'a samo komai kake buk'ata", wani d'an murmushi Sir Benjamin ya saki ya sake kallon P'A ya ce "kuna gama aiki ka turo account zan saka maka kud'in duka". Har suka isa wajan gari sosai zasu nufi estate d'insu, Sir Benjamin ya dakatar dasu yana ma P'A d'insa su juya su koma cikin gari gidansa na hutawa zasu je har zuwa sadda zai kammala aikinsa. Kamar yadda P'A yayi al'k'awari hakance ta kasance an samo jarirai koma nan take aka masu yankan rago, dandanan aka tsutse masu jinin jikinsu. Y'an matan ma an samo su. Sir Benjamin yana zaune daga shi sai wata y'ar rika da gajeran wando, P'A d'insa ya shigo tare da y'an matan da aka samo, su biyu ko wacce ta ci wanka na k'in k'ari suna shigowa wata mai suna Luba ta kalli y'ar uwarta tana zare ido ta ce "Zainab ki duba fa da gaske wannan mutunan wajan president ya kawo mu, wow gaskiya yau mun fito da sa'a zamu samu mugan kud'i". Murmushi Zainba ta saki tana cewa "tabbas duk da ban tab'a ba wani d'a namiji kaina ba sai dai ayi d'an tab'e-tab'e, amma president da kansa dole na basa kaina, Luba kallesa fa da kyau ya had'u over", wani lashe baki Luba tayi tana lumfashe ido yadda take k'arema Sir Benjamin kallo. Tabbas Sir Benjamin kyakkyawa ne na gidan gaba ma kuwa, domin kyansa ne Captain Henry ya gado, sai yazo yama fi Sir Benjamin d'in kyau shi yasa da yawa y'an mata ke hauka akan sa. Cike da yanga da jan hankali suka nufi kan kujeru suka zauna, bayan P'A ya fita yana wani mugun murmushi yana cizo yatsa yana cewa a zuci "zaku ci ubanku ne koba y'an iska ba". Cike da jan hankali Luba ta matsa sosai kusa dashi ganin yadda yake jifarsu da wani irin murmushi mai zautar da zuciya, ai ko Zainab bata san sadda ta d'are akan cinyarsa ba. Ya fara basu wasu zafafan kiss a tare. K'arshe dai suna ji suna gani da mugunta ya rabasu da mutumcinsu, tun suna marmarin abun har suka dawo kuka da magiya ya kyale su, haka nan sun gaji, amma ina sai da suka kai basa ma iya d'aga hannunsu tukun abunda ya k'ara basu tsoro da haushi yadda yake saduwa dasu ta duburarsu, ya sauka daga kansu, tare da d'auke jan kyallen daya shinfid'a a kai a sadda yake masha'arsa dasu. Sai da yayi wanka ya fito, suna zaune da kyar suke zama ma, sai faman share hawaye suke, sun d'auka yana fito zai sallamesu amma suka ga sab'anin haka. Zaro ido Luba tayi jin Sir Benjamin yana waya yana sanar da P'A d'insa ina wuk'ar da kwaryar da zai tari jinin dasu, ya gama aiki na farko ya shigo da kayan aiki na biyu. Su duka cikinsu ne ya fara wani irin kuka na tsabar tsoro. Da mugun sauri Luba ta mik'e bakinta na kyarma wajan furta "mimm miiiimiiii kake nufi ne wai ka sallamemu mu tafi" Wani kafurin murmushi ya saki yana dubansu ya ce "mi kuke ci na baka na zuba yanzu zaku tafi ai inda ba'a dawowa", ya idasa maganar yana sakin wata dariyar ta zallar mugunta. Zainab da Luba ko zaro ido suke kamar kwayar idonsu zata fad'u k'asa bakinsu na kyarma a tare suna kiran sun shiga uku. A sadda P'A ya shigo rik'e da sharb'eb'iyar wuk'a tare da wata kwarya rik'e a hannusa, sai dai kamin P'A da Sir Benjamin su ankara tuni Luba ta tashi a zabure ta fisge wuk'ar dake rik'e a hannun P'A tana nufar Sir Benjamin gadan-gadan da ita a zuciye tana zuwa ta cak................. *Laifin dad'i aka ce k'arewa gamai buk'atar cigaba da karanta wannan BOOK mai suna SAKAMAKO ZUNUBI, zai biya Naira D'ARI BIYAR NE #500 kacal* Zaka iya turo kud'in ka ta wannan account d'in👉 8130479973 Fatima Rabi'u Opay bank Zaka iya turo shaidar biyanka ta wannan number d'in👉 08130479973