UKU BALA'I NA. KAMAL MUHAMMAD LAWAL. (KAMALA MINNA.) 07039355645 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA DAYA. 2018. Jikinta ba abin da yake yi sai rawa kamar wacce ake kaɗawa gangi, ko wacce ruwan sama yayi wa dan karan duka na kin karawa. A hankali ta isa kofar dakin, kallo daya za ka yiwa fuskarta, ka tabbatar akwai kayan damuwa a tattare da ita. ba ma na damuwa kadai ba, har da na tashin hankali. idanuwanta sun kaɗa sun yi jajir. kamar wacce kayi wa surace da hayaki kwalla sun cika su. A hankali ta sa hannunta mai kyarma ta yaye labulan dakin, gami da sallama da fadawa cikinsa. Goggo Marka dake zaune tana faman kaɗin zare. da sauri ta dago ta dubeta, cikin yatsine fuska da tukuicin harara, ta mai da kanta ga kaɗin ta. Mareeya dake tsaye cikin rawar jiki, ganin irin kallon da Marka tayi mata ya fadan mata da gaba, ta san dama a yi haka. harara da yatsinar fuska a wajan Goggo Marka tamkar a jininta yake, in dai ta zo wajanta sai tayi mata haka, ta rasa dalili? tunaninta dai ya tsaya a haka yanayinta yake. amma in tayi duba sai ta ga ita kadai da Ummarta take yi wa haka. nisawa tayi, a lokacin kwallar da ta taru mata a idanu ta zubo. "Goggo. Umma ta ba ta da lafiya tun jiya da dadddare...". Wani kallo ta watso mata, kafin ta saki zaren kaɗin da take yi. ta zabga tagumi kamar wacce akayi wa mutuwa, ta kure Mareeya da kallo kafin ta numfasa. "sai kuma aka ce maki don bata da lafiya ni ce zan bata lafiya ko?. wai ke Mareeya wacce irin dakikiyar yarinya ce? ke a kullum sai kin nuna duhun kai irin na uwarki da kakanninki. in dai za kiyi abu ko". Kwalla ta ciko mata, cikin nisawa. "kiyi hakuri Goggo...". "...ke dalla rufe mani baki, kuma kiyi maza ki fice mani daga daki, kafin na tashi na mangare ki. ban za kawai, jikan yar masu duhun kai, kai jama'a! Allah ya wadaran naka yalalace. nikam! Marka ina ganin kuturun kinibibi wajan nan, yarinya ki marere ce sai faman ɓari kike, ke mai uwa, kin zo sanar dani bata da lafiya, ko uban me zan mata ban sanin miki ba". kara narkewa tayi, kamar zata zube mata a kasa. izuwa lokacin hawaye sun fara zubo mata, ta shiga hada hannayenta waje guda bakinta na rawa. "Ki taimaka Goggo na rokek...". Mahucin da ke kusa da ita ta dauka ta cillo mata shi, bai dire a ko ina ba sai saitin bakinta, hakan ya sanyata gimtse sauran maganarta ta. jin zafi da tayi ya sanyata saurin kai hannu ta dafe bakin ta wani zugi da raɗaɗi take jin laɓɓanta sun dauka, kamar za su fice daga mazauninsu. Da sauri ta juya ta fice daga cikin dakin, cikin yanayi na raɗaɗin zuci da na laɓɓa. ta rasa abin da tayi wa Goggo Marka, take nuna mata halin-ko-in-kula, ta rasa mai ta tare mata cikin duniyarta, ta rasa mai yasa ta ke nuna musu kiyayya ita da uwarta. tun da take da ita daidai da rana daya bata taba jin ta furta kalma daya akan taba ko uwarta, mai dauke da Alheri. kullum aikin ta kenan nemo inda aibu yak,e ta makalawa rayuwarsu. ita dai tunda ta taso ba ta ga uwarta na nunawa Goggo Marka, wani halin rashin girma ko na cin mutunci ba. kullum cikin biyayya da girmamwa take. amma duk wannan bai hana Goggo Marka ci mata mutunci ba a gaban kowa, ko da kuwa gaban Babanta ne. Kuka takeyi wanda bashi da sauti ko kadan, illa hawaye da suke fitar burgu daga idanuwanta, tana faman dauke su amma kamar kara tunkudosu ake. tana jin zafin zuciya da yarda kasar ruhinta ke raɗaɗi, idanuwanta in da sabo ya ci ace sun saba da halin da Goggo Marka, ke nuna mata ita da uwarta. A hankali ta karasa dakin mahaifiyarta. kafin ta shiga sai da ta dauke hawayen fuskarta kaf. domin bata bukatar mahaifiyarta ta taga halin da take ciki, hakan zai kara tayar mata da hankali sosai. kofi ta dauka bisa randar ruwan dake kofar dakin, ta debo ta wanke fuskarta, sannan ta sanya haɓar zaninta ta tsane fuskarta tas. amma hakan bai hana a gane tayi kuka ba, domin idanunta sun kaɗa sunyi jajir, murmushin yaƙe ta kalato ta yafawa fuskarta, sannan ta shiga cikin dakin bakinta dauke da sallama. Tsaye ta hango uwarta ta, sai faman hada gumi take yi tana kai kawo. kallo daya zakayi mata ka tabbatar tana cikin matsanancin yanayi, lakari da yarda take cizon laɓɓanta kamar zata cizgesu daga mazaunansu. fuskarta ta rine tayi jajir abin ka da farar mace. kallo daya Mareeya tayi mata ta kau da kai, jin kuka na shirin kawo mata ziyara, zuciyarta ta shiga bugu. ta sani uwarta na cikin yanayi na matsaninin ciwo, amma ta rasa mai ya kamata tayi domin taimakon, ta a matsayinta na 'yarta wacce ta haifa a cikinta. waje daya taje in da take tunanin za ta samu waraka, amma anyi mata korar kare tare da bakaken maganganu. "Mareeya ya akayi na ganki haka, mai ya sameki?". Habeeba ce ta fadi haka, cikin karfin hali da na zuciya. sai faman numfarfashi take, gumi na cigaba da karyo mata, kamar wacce ake juyewa bokitin ruwa. yanayin sautin muryar Habeeba da maganarta, ba karamar rauni suka kaiwa zuciyar Mareeya ba. ji take kamar ta rushe da kuka saboda tsananin tausayin uwarta. jin amonta ya tabbatar mata tana cikin wani mataki mai tsananin wahalar da rai da ruhi, ta sani uwarta tana hakuri tana da juriya, da alamun a wannan fikirar hakurinta da juriyarta ba za su samu muhallin zama ba. Juyawa tayi, ta fuskanci mahaifiyarta sosai. tana faman gyaɗa kai cin yanayi na tausayawa. "lura da nayi da halin da kike ciki, ya sanya ni zuwa neman wani taimako daga wajan Goggo. amma hakan bai samu ba". ta karashe tana goge hawayen da suka zubo mata, tana jin yarda zuciyarta da kasar ruhi ke tsalle-tsalle cikin yanayi na tausayi da neman wata hanya domin samun mafita. Habeeba ta gyada kai, tana mai sakin murmushi wanda daka kalla zaka san na dole ne, ba wai don wani farinciki akayi sa ba ko na tsuwa. to ina ma natsuwar take wacce ta rigaya ta falle da gudu ta bar duniyarta. "Hmmm Mareeya kenan. kuma don kin je ba ta aminta ba shine ki kayi kuka?". Ta karashe tana mai kafe da kodaddun idanuwanta, wanda suke cikin hali na rashin nutsuwa. Girgiza kai Mareeya tayi kafin ta dubi uwarta ta, murya da salon rauni. "Umma gani nayi ita ce kusa damu shiyasa na yi tunanin ita yafi dacewa aje wajanta, ba wai aje waje ba. kuma gata a cikin gida, sai nake tunanin in har aka je waje aka nemo a matsayinta na babba ba za ta ji dadi ba. ashe ba haka bin yake ba, tunani na daban da hasashena akanta". ta karashe cikin rawar murya, mai son fashewa da kuka. a daidai lokacin ta ga uwarta ta, ta saki wani nishi wanda ya taho da wasu tawagar hawaye, da hanzarinta ta isa gareta, ta riko mata hannu. "Umma ko Asibiti zamu tafi, Umma ko naje na kira Baba ne?". Abin da ta shiga fadi kenan, cikin yanayi na bugun zuciya, mai tattare da tsoron halin da ta ga uwarta ta aciki. bata tanka mata ba, illa numfashi da take ta faman ajjewa. lokaci lokaci hannunta na kan turtsetsen cikinta, wanda take jin duk wani hali da take ciki na wahala shine sanadi. shine yake rangwantar mata da jarumtar ta, ya ke rangwantar mata da kumajinta, da duk wani azanci nata. Girgiza kai ta shiga yi, alamun a,a ba sai ta je ba. hakan ya kara rudar da 'yar natsuwar Mareeya, nan ta shiga girgiza kai, ita ma tana sakin nishi mai dauke da son fashewa da kuka. "a,a Umma. karki ce haka don Allah, kina bukatar taimako a halin da kike ciki, don Allah ki yarda a nemo mai taimaka miki ko kuma mu tafi asbiti".. Girgiza mata kai ta cigaba da yi, tana jin wani irin ciwo mai tsananin karya jarumtar numfashi na kawo mata farmaki, ji take kamar numfashin ta zai katse, duniyar taji ta shiga juya mata kamar zata jirkitar da ita, ba abin da take ambato a ranta da kasar ruhinta sai 'Innalillahi wa inna ilahir raji'un'. Hawaye suka shiga digo mata wanda take jin su kamar garwashin wuta ne ake goga mata a fuska, hannun Mareeya ta rike gam! kamar zata tsinke shi, ita kanta Mareeya taji rikon da uwarta ta tayi mata, sosai da sauri ta dago kai ta dubeta, idanuwanta sai hawaye da suke digo. "Umma ki ce wani abu nasan kina jin zafin ciwo sosai, don Allah ki bani izinin zuwa nayi wani abu, rayuwarki tana da matukar muhimmanci a duniyata". Izuwa lokacin Habeeba hayyacinta ya fara raguwa da ga gareta, kafafunta da take kansu suke taimaka mata wajan tsayi, ji tayi suna karkarwa alamun sun fara gajiya da rikita. Da sauri ta ja jiki zuwa kasa, tana dafa Mareeya ta zauna kan lamusshasshiyar katifar dake yashe tsakar dakin, har zuwa wannan lokaci idanuwanta a rufe suke, ita kadai ta san irin raɗaɗin azabar da take ji, ita kadai ta san irin zafin da take ji yana ziyarta ta. ɗan dake cikinta tana jin yarda yake juyi cikin wani irin yanayi na hanzari, yana tunkuɗo mata gurbin zuciya, ji take kamar zai tarwatsa mata kirji, zillo yake yi ta ko ina yana bugun ko wani sashi na cikin ta, ba abin da take hasashowa kanta a wannan matakin sai ficewar rai, domin ta gama yarjewa zuciyarta SILAR AJALINTA ya zo cikin duniyarta, matakin daukewar numfashinta ya iso rayuwarta, barin duniyar rayuwarta cikin yan dakiku take hangowa, lahirarta tana yi mata maraba lale, duniyarta nayi mata ban kwana. Wani zillo da taji ɗan cikin nata yayi, da sauri ta durkushe bisa gwuiwowinta, tana faman sakin wahalallan numfashi wanda take jin fitar sa ma, wani raɗaɗi yake haifar mata a ruhi. Sake damke hannun Mareeya tayi, wacce a wannan lokacin hawaye kawai take saki, tana kallon yarda mahaifiyarta ke yi cikin wahalallan yanayi ba abin zuciyarta ke hasaso mata sai uwarta ta mutuwa zata yi. "Umma sakar min hannu don Allah, naje na nemo mai taimaka miki kinji". ta fadi cikin murya mai dauke da rawa da kuka a jikinta, ta shiga faman jan hannunta, domin kwacewa amma ina!. rikon da tayi mata ba mai sauki bane, kuka ta saki sosai tana jinjiga uwarta ta, tana rokon ta da ta sake ta, domin zuwa kiran wani ya taimaka mata. A hankali taji hannun uwarta ta na buɗewa daga rikon da tayi mata, cikin yanayi na rashin karfi jikin. sagalo tayi tana kallon hannun nata wanda cikin dakiku ta sakar mata shi, hakan ya kara mata jarumta, da sauri ta mike har tana cin tuntube zata zube kasa, ta fice daga cikin dakin. ba in da ta dosa sai dakin Goggo Marka, ko sallama ba tayi ba, ta fada dakin ta zube a gabanta, har wannan lokacin ta nan tana aikin ta na kaɗi. ganin Mareeya zube a gabanta ya sanyata tsayawa cak! da abin da take yi. tana dubanta cikin haushi ji take kamar ta kwasheta da mari, hannu ta shiga nuna mata. "Mareeya so ki ke yi ki nakasta ni, zaki fado min kai haka kamar buhun maiwa". cikin kuka Mareeya ta dago kai, gami da riko kafafuwanta. "kiyi wa Allah Goggo ki taimaki Ummata karta mutu, na roke ki". Fincike kafarta tayi, gami da mikewa tsaye tana gyara daurin zaninta. "kar uwarki ta mutu ko? wai shin in naje ni zan hanata mutuwa, ko ce miki akayi ni ce mala'ikan daukar rai ga mutum, kisan Allah in har baki tashi kin fice daga cikin dakin nan ba sai na karyaki, banza 'yar masu duhun kai". Kuka take yi na zuciya har izuwa kasan ruhi, ji take yi zuciyarta na raɗaɗi gami da zafi, idanuwanta suna zugi gami da zubda zafafan hawaye. jikinta na rawa da karkarwa duniya gabadaya taji tana kai kawo da ita, ba abin da take hasasowa sai yanayin da mahaifiyarta take ciki, ta tabbata a wannan yanayin da take ciki bashi da maraba da hanyar mutuwa, duk da dai ba ta san ya ake mutuwa ba, amma ta san hanyar mutuwa ba dadi gareta ba. Mikewa tayi tana duban Goggo Marka cikin hawaye. "Goggo na roki da Allah da Annabi ki taimaka ma Mahaifiyata. ina rokonki ko da wani abu tayi miki wanda kike ganin ba zai sa ki taimaka mata ba, to ina so duk wani hukuncin da zuciyarki ta yarje miki kiyi akan ta to ya komo kai na. ni dai alfarma nake nema ki taimaka mata ba don halinta ba". Sagalo tayi da baki tana kallonta, in ka ganta sai ka rantse tausayi da jin kai ne ya sanyata haka. amma saboda rashin sanin daraja sai ta sake kwaɓe baki gami da kau da kai. "ina gani bariki yau, ke yanzu Mareeya har kin yi girman da zaki sakar min magana haka to bari kiji ko Malam Lamiɗo (tana nufin kakan Mareeya) bai isa ya zo ya sani abin da ban yi niyya ba, don haka maza ki tashi ki fice mani daga daki, tun kafin na yi kutubal dake". Hannu ta sa tana dauke hawayen da suke zubo mata, wasu na biyo bayan su tana kallon Goggo Marka kallo ne take yi mata na bakinciki, tausayi da imani sam babu su zuciyarta. gyada kai tayi tana nufi kofar ficewa daga cikin dakin, ba tare da ta sake kallon inda Goggo take a tsaye ba, ta yi sagalo sai faman watsa mata kallon banza take yi. Zuciyarta tayi matukar yin baki gami da kuntata, zafin rai da take ji yana ziyartatta ya sanyata sakin wani kuka mai dauke da tashin hankali da takaici da baki ciki. Tsakar gidan ta tsaya, ta durkushe tana faman rerashi wanda ba shi da sauti, in ba kana kusa da ita bane ba za ka taba gane kuka takeyi ba. ta jima durkushe a wajan, domin rashin abinyi gabadaya kwakwalwarta ta cushe, ta rasa ina zata dosa, ta rasa meye abin yi, za ta so ace asibiti suka tafi kila can su samu taimako, sai dai ba anan gizo ke saƙar tasa ba, domin zata iya ratsewa rabon da suga naira biyar cikin dakin su mallakinsu ko ta ajiya sun fi karfin mako daya, to ina batun in sukaje asibiti ta sani kudi za a nema kafin ma akula mahaifiyarta ta shi kuma mahaifinta ba ta san inda zata same shi ba, rabon ta dashi yau kusan kwana uku kenan. ba ta san gun wanda za ta ba, ba su da yan uwa nan kurkusa balle taje domin su share musu hawaye, ba dangi wanda za ta ce gashi anan kusa wanda zai taimaka musu, ba ta san kowa ba, ba ta san gun wanda zata je ba, tunaninta ya tsaya cak ba ta da wata mafita. Kamar daga sama taji an dafa mata kafada, cikin hanzari ta dago fuskarta shaɓe-shaɓe da hawaye, mahaifinta ta gani wata irin zabura tayi, ta mike tana kallonsa. hannunsa ta rike jiki na rawa. "Baba Ummata ka taimaka min, za ta mutu na roke ka". Yanayin da ya ganta ya san shi saurin riko mata kafadu yana girgizata. "mai ya sameta, tana ina?". baki na rawa ta nuna masa daki. da hanzari ya nufi dakin yana mai rike da hannunta suka yi dakin. duk abin da suke yi Goggo Marka na kallo, tana laɓe jikin labulan dakin ta tun da taji muryar Adamu ta leko tana ganin sun shiga dakin, ta fito tana murmushi ita ma dakin ta nufa, cikin hanzari yanayin da ta nuna a jikinta sai ka rantse da gaske taimakon za ta je yi. Yana shiga ya tadda ta durkushe ganin haka, ya isa gareta da sauri yana ambaton. "innalillahi Habeeba meke faruwa ne, ko haihuwar ce?". ya rikota yana mai girgizata idanuwanta a rufe, ya durkusa gabatan ya tallabo haɓarta. A daidai lokacin Goggo Marka ta iso tana marere cewa kamar gaske, ta isa garesu tana tafa hannu gami da salallami. "me nake shirin gani haka Habeeba meke damuki, baki da lafiya amma ki ka ki sanar dani, haba habeeba sam haka bai dace ba". ta karashe cikin yanayi na rauni da tausayawa, rikota tayi tana mai cewa Adamu. "ina tunanin haihuwa ce ta zo mata". gyada kai kawai yayi cikin yanayi na tsoro da halin da ya ga matar ta shi a cikin, tausayinta ya gama mamaye masa zuciya ya tabbata Habeeba tana cikin mawuyacin hali, lakari da yarda ya ganta aciki, wanda bai taba gani hakan ta faru a gareta ba, zuciyarsa ta shiga bugu da sauri ya dubi Goggo Marka. "ko dai Asibiti zamu wuce da ita". Wata irin zabura tayi jin ya ambaci Asibiti. "haba Adamu haihuwar ce sai mun tafi asibiti, ai ko can muka je in dai lokaci bai yi ba haka zamu ta zama har lokaci yayi, ko kuma su saka karti su ta jagwalgwalata har su yi mata illa ko kuma su dakusar mata da karfin nata, su saka ta haihuwar dole tun lokaci bai yi ba, kadai mu bi komai a hankali, in lokaci yayi zata haihu". ta fadi kamar gaske, tana faman rike Habeeba sai faman sannu take yi mata, sai ka rantse har kasar zuciyarta haka ne. Ba yarda ya iya, haka ya gyada kai shi ma yana faman yi mata sannu. ita kuwa Mareeya mamaki da tu'ajibi ne suka cika ta, ta ma rasa abin cewa, ganin yarda Goggo Marka ta zage tana faman narkar da murya ita ala dole tausayi take ji, kamar ba ita bace ta gama kwashe mata albarka ba yanzu. girgiza kai tayi cikin yanayi na tsanar halin Goggo Marka. "Maza ke kuma ki tashi ki fice daga dakin, kin zauna kin kure mutane da idanu". Goggo Marka ta fadi tana mai duban Mareeya tana galla mata harara ta gefen ido, ba wanda ya kula da hakan sai ita kadai kau da kai tayi, tana duban mahaifin nata wanda hankalinsa gabadaya yana kan matarsa, yana dubanta yana kallon yanayin da take ciki na tsananin wahala, zai so ace sun tafi asibiti da ita yana ganin haka shine kawai yafi dacewa, sai dai maganar Goggo Marka tayi masa katanga da hak,a ba don ya so ba ya dubi Mareeya da take ta faman ajiyar zuciya, hawaye sun cika mata idanu ya ja hannunta suka fice daga cikin dakin, zuciyarta sai faman azalzala take yi da tsoro don tana fargaban barin Goggo Marka da Uwarta ta kar tayi mata wani abu, domin irin kiyayyar da ta hango a idanuwanta komai za ta iya aikatawa. Can nesa da dakin ya ja ta ya zaunar da ita, yana mai rarrashinta da ta bar kuka In Sha Allah uwarta za ta samu lafiya, ita dai gyada masa kai kawai take yi, amma ba ta hango hakan ba. hankalin ta gabadaya ya karkata izuwa wajan uwarta da kuma Goggo Marka da aka bari tare da ita, tsoro take ji. Ba su jima da fitowa ba, Goggo Marka ta fito daga cikin dakin duk ta hada gumi kamar gaske. dubansu tayi gami da rausayar da kai ta wuce dakin ta, an jima kadan ta fito hannunta dauke da kullin abu, ba tare da tayi wa kowa magana ba ta samo kwano ta kwance kullin da ta ɗanko daga dakinta, wasu sauyoyi ne a ciki kwasa tayi ta zuba cikin kwanon mai dauke da ruwa ta shiga jujjuyawa, gaban Mareeya ya yanke ya fadi, ta zaro idanu tana kallon abin da take yi gabadaya hankalinta bai gamsu da abin da take yi ba, nan ta dubi Babanta, shima Goggo Marka yake kallo. sai da ta gama motsawa sannan ta mike ta nufi cikin dakin. da sauri ya tare ta da cewa. "Goggo wannan kuma menene?". Murmushi tayi gami da margaya kai. "magani ne mace dake kan gwuiwa ake baiwa, domin samun sauki da kuma haihu sumulkalau ba tare da an samu matsala ba, yanzu ina bata shi in dai haihuwar ta zo to nan da nan zaka ga ta haihuwa abinta". Ba ta tsaya jin abin da za su ce ba ta fada cikin dakin. izuwa wannan lokacin Habeeba sai faman numfashi take yi da nishe-nishe lokaci lokaci, gumi ya gama game mata jiki gabadaya. isa tayi gareta ta rangwafa gami da tallabo haɓarta dake kasa, ba tare da komai ba ta tura mata kwanon mai dauke da jikanken sauyoyin, wani hamami ne da daci suka dake hancinta da harshenta da sauri ta kau kai, duk da tsananin da take ciki bai hana ta tsanar wannan abin da ake kokarin ba ta ba. Goggo Marka ta na ganin haka ta sake kakaba mata tana mai kashe murya. "hakuri zakiyi ki sha Habeeba, shi zai taimaka maki wajan samun saukin nakudar. duk wani ɗaci nashi daure wa zakiyi haka". ta sake kai maka shi baki nan ma kau da kai ta sake yi, cikin tsananin kin abin ta shiga numfarfashi, a lokacin nakuɗar ta sake motsa mata ji take yi kamar bayanta da kwankwasonta za su karye, ta dago da jajayen idanuwanta cikin rashin hayyaci ta dubi Goggo Marka wacce ta ke ganinta tana kasuwa gida bibbiyu a gareta, ta mai da kanta kasa tana mai sakin numfashi. ita kadai ta san halin da take ciki, ita kadai ta san azaba da raɗaɗi da take ji a kowa ni sashi na jikinta... [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU BALA'I NA KAMALA MINNA. *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA BIYU. Awa daya tsakani amma shiru kake ji, ba wani cigaba wanda za ace na a zo a gani, har hankula su saka ran samun natsuwa. Malam Bello zuciyarsa ta gama karaya matuka, ji da yayi shiru ba alamun haihuwar, anyi ta ko ba ayi ta ba, ya rasa matsayar da zai ajje zancen zucin sa. Numfashi yake ta faman ajjewa, sai ka rantse shima nakuɗar ce akan sa, ya dubi Mariya wacce ta ke cikin yanayi na faduwar gaba da rikitar zuci da ruhi, duk hannaye biyu ta saka ta tallabe haɓarta, idanuwanta sun yi jajir hakan ya kara tsinke masa natsuwar zuciyarsa, sai faman bugu take yi tana yaso masa wani banzan zance wanda ba shi da muradin ace ya tabbata cikin duniyarsa, in kuwa haka ya tabbata ko shakka ba ya yi zai fi kowa ruɗewa cikin duniyarnan. a hankali ya shiga ajje numfashi, yana kallon dakin da Matar tasa take wanda ya tabbata izuwa wannan lokacin mutuwa ta zo kusa da ita. Da wannan zancen zucin ya kokarta mikewa yana faman hirji kamar zai ci babu, ya doshi dakin cikin bugun zuciya da ruhi. Yaye labulan yayi cikin rashin tabbacin abin da zai gani, duk da dai zuciyarsa tana yi masa kuwwa akan ba sauki sai wajan Allah. idanuwa da numfashinsa gami da bugun zuciyarsa a lokaci guda suka shiga rudu, ganin yanayin da ya ga Habeeba a ciki, da hanzari ya fada dakin ya dubi Goggo Marka, wacce ke zaune can gefe ta zubawa Habeeba idanu, ba wani alamun tashin hankali tattare da ita, maganar Malam Bello ne ta dawo da ita duniyar rauni, da kokarin yafawa fuskarta yanayin tausayi, ta shiga duban shi. "ka gani ko, har yanzu ba alamun haihuwar ina ga dai lokaci ne baiyi ba, ko kuma juyi ne". Ta fadi cikin yanayi na kara narkewa a tausayi. Gyada kai kawai yake yi, kamar wani kadangare yana faman jan numfashi yana ajjewa, idanuwansa da hankalinsa har da natsuwarsa duk suna kan matar sa, sake ajje numfashi mai kauri yayi. "Goggo kawai mu tafi Asibiti". ya dasa aya yana kokarin isa wajan Habeeba. Da sauri ta tare shi. "a,a mana Bello, mai yasa zaka nuna gajen hakuri ne, na fada maka in haihuwar nan ta zo yin ta za ayi, amma na ga alamun taurin kai za kayi. haba don Allah ko fa Asibitin muka je hakance zata kasance". Bai amince ba, bai yarda ba da maganar ta sam. bai hango ɗa mai ido ba cikin wannan lamarin, don haka ya dube ta sosai, cikin karyar da murya. "Goggo zuwa Asibitin shine ya fi dacewa, domin zaman gidan ba karimin hatsari zai farar ba". Duban sa tayi, cikin shan kamshi. "me ka ke nufi Bello, kana nufin a matsayina ba zan iya amsar haihuwar ba ne ko yaya?". Girgiza kai ya shiga yi, cikin yanayi na rashin natsuwa. "ba haka bane Goggo, ya kamata ki fahimta wani abu, kin ga can asibiti in muka je ko ba haihuwa ba ce su sun san abin da ya dace suyi mata, domin ganin komai ya zo yarda ya dace, amma zaman gidan ba abin da zai haifar sai dai ya je fa mu a ruɗu da rashin abin yi kawai, sai dai mu sata gaba muna kallo". "ba in da za a kai ta Bello, na fada maka ka duba fa ka ga yanayin da take ciki, alamun ya nuna haihuwar gaf take da yin ta yanzu, in muka dauke ta cikin wannan halin komai zai iya faru a hanya, za ta iya haihuwa a titi me kenan akayi?". ta fadi cikin yanayi na rashin jin dadin maganganunsa, ta yafa wa fuskarta yanayin kamar gaske ta shiga cizon laɓɓa, sai ka rantse zage ta yayi tas. Wani marainin nishi Habeeba ta saki, wanda da kaji amonsa kasan wahala ce tsagwaronta ba mis a cikin ta, hakan ya kara ruguza 'yar natsuwar Bello, ya shiga dubanta sai faman fadin "Sannu" yake yana ji azuciyarsa har da can kasar ruhinsa kamar bai yi mata adalci ba, in har ya yarda da batun Goggo. sai dai kuma a wani bangaren in ya ki amsar maganar Goggo, kamar kin biyayya ce a gareta. duban Goggo yayi ya sake juwa wajan Habeeba, wanda ko tantama ba yayi mutuwa tana kurkusa da ita, in kuwa mutuwa ba ta zo ba to tabbas bakar izaya da wahala tana ɗawainiya da gangar jikinta da zuciyarta. "kiyi hakuri Goggo, mu kai ta asibiti...". Wani kallo ta watsa masa, kafin ta fara magana cikin ɗaci. "wai shin in tambayeka yau ta fara haihuwa ne a duniyarta, na dauka ta haifi Mariya kuma a gidan nan ta haifeta, ba tare da zuwa wani waje ba. to bari kaji na fada maka ba in da zata, a gida zata haihuwa kana kallo fa na bata magani rage zafin nakuda, da zuwan komai a sannu kuma da ka kalle ta za ka san maganin yayi aiki..." Da sauri ta katse batunta, lokacin da taga wani ruwa ya fara gangarowa daga kasan Habeeba. "ka gani ko. har faya ta fashe haihuwar ma ta zo nan kurkusa, sai ka fice ka bamu guri ko a nace". Ta kareshe tana galla masa harara. da sauri ya dubi Habeeba, yana kallon yarda ruwan da bai san na menene ba, yake zubowa daga jikinta wanda ya tabbatar da zancen Goggo din, amma bai amincewa kan sa ba, har can kasar ruhinsa. ba yarda ya iya haka ya fara jan jiki yana kallon Habeeba, yarda take wani irin nishi da murkususu kamar za a zare mata rai. Zuciyarsa ta kara yin rauni, ganin yarda Habeeba ke shan wahala. in da yana da yarda zai yi da ya dauke mata wannan azabar ya daurawa kan sa, amma ina! ba hali, haihuwa mace ce kawai take da wannan alhakin nayin ta, wanda ba komai bane a cikin ta sai tsatsar azaba da wahala, tausayinta ya kara tsargar masa a jiki. da wannan yanayin ya isa inda Mariya take zaune, ta na ganinsa ta mike idanuwanta akansa, sai nar-nar suke alamun son zubda hawaye, tana kokarin yin magana ya yi saurin riketa ganin kuka na kokarin kufce mata, ya shiga girgiza kai kamar wani d'an kadangare. "karki yi kuka Mariya, komai tsanani yana tare da sauki da yardar Allah, kuka sam bai ka mata ba..." da sauri ta tareshi, tana mai gyada kai, hawayen da take boye su suka shiga zubowa, kamar an murde kan rubabben famfo. "Abba Umma ta ina son ta, bana so na rasata don Allah ka taimaka mani ka taimaka mata, mu kai ta asibiti kar ta mutu ta bar mu cikin duniyar nan, ba zan iya rayuwa ba na rokeka". Ta karashe tana mai zubewa a kasa, kamar wacce aka bugewa gwiwowi ta shiga sakin kuka mai cin rai da tsuma zuciyar mai sauraro. Kallonta yake yi, cikin wani irin hali na tausayawa zuciyarsa gabadaya ta gama raunacewa ji yake yi kamar ya daura hannu saman kai, ya zunduma ihu. wani radadi da zafi gami da zugi yake ji suna taso masa, tun daga kasar ruhi har zuciya gabansa sai amsa wani irin bugu yake yi mai dauke da kayan tashin hankali cikin sauri-sauri. dafe kai yayi da duk hannayensa ya rasa mai ya kamata yayi, ya rasa mai ya dace yayi, domin samo mafita akan wannan lamarin dake kokarin janyo masa tashin hankali. ya rasa da mai zai ji, ya sani Habeeba na cikin halin wahala dole ya nemi mafita, dole ya kai ta asibiti, in da yake tunanin nan ne kawai ya dace ace a halin da take yanzu tana can. sai dai wani hanzari ba gudu ba, Goggo Marka ta hana yin haka, ya rasa mai yasa ta kasa fahimtarsa, ya rasa mai ya sa taki yarda ta amshi rokonsa, ya rasa mai yasa take kokarin janyo masa abin da zai haifar masa da tashin hankali, taki fahimtarsa, taki gane matsalar da yake hangowa za su fad'a, ya kamata ta fahimta zamanin da da yanzu ba daya bane, komai ya sauya kamar yarda komai na cikin duniya ya sauya, haka zamani yake sauyawa da abubuwa masu dauke da karin haske ga duniyar dangin rai sai dai taki amincewa da cewa ZAMANI YA CANZA. "Abba don Allah kar ka bari maganar Goggo tayi tasiri a zuciyarka, har ta hanaka ceto rai". Mariya ta fadi cikin rawar murya, tana duban mahaifin na ta, cikin kasalallan yanayi. Gyada mata kai ya shiga yi, kafin ya ja jiki ya fice daga cikin gidan, ya bar ta nan tallabe da haɓa. Bakin titi ya nufa, mai Napep ya dauko ya dire kofar gidan, ya ce dashi ya jira shi cikin gidan ya fada cikin jarumar zuciya, a daidai lokacin Goggo Marka ta fito daga cikin dakin a firgice saura kadan suyi karo, idanu ya zuba mata yanayin da ya ganta ya sanya gabansa tsananta bugawa, ita kanta Mariya ba karamar razana tayi ba da sauri ta bi bayan mahaifinta, ganin yanayin da yake ciki yana fadawa cikin dakin yayi daidai da karar da Habeeba ta saki, gami da bingirewa jini na malala ta karkashin ta, ga kan jariri ya yo waje bai san lokaci da ya isa gareta ya durkushe gami da tallabo haɓarta, zuciyarsa ta buga lokaci guda ganin da yayi ba alamun numfashi a jikin ta, hakan ya kara masa firgici, zabura yayi gami da ficewa waje, cirko-cirko ya tadda da su, Goggo Marka tallaɓe da haɓa kallo daya zakayi mata ka hango rashin gaskiya da firgici kwance a cikin idanuwanta, ita kuwa Mariya hannu ta daura akai ganin yarda mahaifinta ya fito, ta kurma ihu gami da zubewa kasa tana fadin. "Shikenan rayuwa ta gurgunce a duniyata, shikenan na bani na lalace a rayuwar duniya, shikenan tsanin rayuwata ya karye...". Da sauri ya isa gareta, ya dago ta. "Mariya daina fadin haka, wa ya sanar dake ta mutu, ta na nan da ranta". ya fadi yana mai juyar da kallon sa wajan Goggo Marka da tayi wuki-wuki kamar wacce tayi wa sarki karya, girgiza kai yayi, da sauri ya koma cikin dakin dalilin wasu lamura da zuciyarsa da kwakwalwarsa suka shiga sanar dashi, cikin jarumtar zuci da na jiki ya shiga gyara mata jiki, idanuwansa cike da hawaye ya dagota gabadaya ya rungume ta, ya fice daga cikin dakin cikin hanzari ba in da ya direta sai cikin Napep, shi kansa mai Napep din ya tsorata da yanayin da ya ganta aciki, da sauri ya shiga ciki gami da tayarwa, Malam Bello gabadaya ya gama ficewa daga hayyacin sa. kwalla da suka taru masa a idanu sai shatata suke kamar wani karamin yaro. har Napep ya fara kokarin tafiya, sai ga Mariya ta fallo a guje tana kuka, tana mai cewa da mai Napep din ya tsaya don Allah, amma Malam Bello ya ce su tafi kawai don yasan in har Mariya ta biyo su, kafin su kai sai hankalin su ya kara tashi musamman in da take nan a firgice, yana hangota tana daga masu hannu tana kiran su cikin muryar kuka. kai ya shiga girgiza mata, yana mai daga mata hannu alamun ta koma gida. amma ina kuka ta sake rushewa da shi gami da durkushewa, ta saki wani sabon kukan mai cin rai da tsuma zuciya, kuka take yi kamar ranta zai bar jikinta, wani zafi take ji tun daga kasar ruhinta har zuwa inda zuciyarta ke ajje. ta gama yanke tsammani akan sake ganin mahaifiyarta a duniyar rayuwarta dauke da numfashi, zuciyarta ta gama yarje mata sun yi rabuwa kenan har gaban abada, ba za su sake haduwa ba. ta ji ma cikin wannan halin. kafin ta kokarta cikin jan jiki ta mike tana faman tangadi, duniyar gabadaya ji take tan juya mata, komai ya kwance mata, komai ya lalace cikin duniyarta, kayan farinciki tuni suka guje suka barta, ji take kamar zuciyarta zata tarwatse, kwakwalwarta ta na faman kai kawo cikin duniyar tashin hankali da rashin tsammanin samun sa, sannu a hankali take tafiya idanuwanta a rufe jefa kafa kawai take yi a duk in da taji kafar ta ta, ta bata damar haka, cikin ikon Allah ta isa kofar gida, tana kokarin sanya kai cikin soron, sukayi karo wani irin zafi da raɗaɗi ta ji goshin ta ya dauka, da sauri ta buɗe idanunta tana dafe goshinta, wasu zafafan hawaye suka zubo mata. Goggo Marka. ta gani tsaye idanuwanta akan ta, sai faman tsume fuska take yi. kau da kai Mariya tayi, tana mai jin zafi rai suns dago mata da duk wani numfashinta, ta fara kokarin rakuɓeta za ta wuce, wani wawan cafka ta yi wa wuyanta, ta dawo da ita gabanta. "ke mai uwa ko, shine saboda rashin sanin darajar kai, ki ka zube a titi kina kwarar baki. to dan uban ki in ba duniyar kika dauke da ihu ba, za a kashe miki uwa ba ki cika Mariya jikan Lamiɗo ba shegiya bakar munahika kawai. Girgiza kai ta shiga yi,hawaye na sake balle mata sam maganganun Goggo ba su taba mata zuciya ba, domin tashin hankalin da take ciki ya zarce duk wata bakar magana ko zagi da za ayi mata, hannu ta sanya ta dauke hawayen da suka cika mata idanu ba tare da ta sake bin ta kan Goggo ba, ta sake yinkurin shigewa cikin gidan. a wannan karon ba ta hanata ba, sai kwaɓa da tsaki da ta bi ta dashi. Tunda suka dauki hanyar Asibiti, Malam Bello ke rungume da Habeeba. ba abin da yake yi sai zubar hawaye, har zuwa wannan lokaci jini bai daina zuba a jikinta ba, gabadaya shimfidar cikin Napep din ta baci shi kasan direban lokaci-lokaci yana juyowa ya dube su, domin ba karamar firgita yayi ba, sai faman zabga gudu yake yi kamar zai tashi sama, burin sa kawai su isa Asibiti, domin ceto ran Habeeba. Mintina goma kacal ya kai su Asibitin baban alis, yayi Parking gami da direwa, da gudu yayi cikin Asibitin yana mai sanar da Nurses su taimaka wata ce ba ta da lafiya, yanayin da yake ciki na rashin hayyaci, sai ka rantse uwarsa ce ba lafiya amma Nurse din ba wanda ya bi ta kasan, kowa harkar gabansa yake yi, mutanan da suke zazzaune sai faman bin sa da kallo suke, cikin yanayi na tausayi, domin sun tabbata ba abu ne mai sauki zai firgita duniyar tunanin wannan matashin ba. tun yana neman daukin su, su kula shi amma ba wacce ta kulashi, sai da ya isa kusa da wani teburi ya shiga duban matar dake zaune, ta na ba da katin ganin likiti, ya dubeta. "don Allah ku taimaka likita, haihuwa za tayi jini na ta zuba a jikinta". dago kanta dake sunkuye tayi, tana dubansa cikin gilashin dake fuskarta. "ka je ku shigo da ita, sannan kuma ku kawo katin da take zuwa awo dashi, domin ba za a taba ta ba, har sai an bada kati". da mamaki ya shiga dubanta, ganin yarda ta nuna halin ko in kula akan lamarin. ji yayi kamar ya dauke ta da mari, amma ya kasa. da sauri ya juya zuciyarsa na zafi da radadi irin yanayin da ya ga Nurse sun nuna masa, da sauri ya isa wajan Napep, ya tarar Malam Bello, na kokarin fito da ita wacce a wannan lokaci kallo daya zaka yi mata, ka bawa zuciyarka amsa cewa ba ta da rai. Cikin Asibitin yayi da ita tana rungume a hannunsa, mutane da yawa sun tsorota matuka da yanayin da suka ganta, suka shiga sallallami suna zaro idanu, Malam Bello, da ke rikice ya rasa ma in da zai yi da ita, sai faman zarya yake yi magana ma ta gagare shi, duk abin da yake da yawa Nurse na kallon sa, amma sai dai su ba banza ajiyarsa. ciki mutanan dake zaune a harabar asibitin wasu mata biyu suka iso gareshi,tare da taimaka masa, zuwa daya daga cikin dakin Asibitin. a daidai lokacin Nurse mai siyan da kati ta iso cikin dakin, tana duban Malam Bello. wanda gabadaya ya gama yin nisa da hayyacin sa. tambayarsa take, amma ya rasa bakin bata amsa, sai motsi yake yi da baki, daya daga cikin matan da suka taimaka masa ne ta dubi Nurse din. "wannan ba fa shi ne mafita ba, ya kamata ko taimaka mata ki duba halin da wannan baiwar Allah take ciki, mana maganar kati duk ba shi da muhalli a halin da ake ciki, ceto ranta take bukata". Kau da kai tayi, tana mai ya tsine fuska. "ke ma kin san haka ba za ta taba yuwuwa ba, dole sai da katin ta na shaidar ta na zuwa ganin likita, sannan za a kula da ita". Ta karashe maganar ta tana kokarin ficewa. da sauri dayar matar wacce da alamu haushi ya cikata, ta sha gabanta tana yi mata kallon na raina matsayin ki. "wai ke kuwa kina da ita imani, baki san zafin da raɗaɗi bane a wajan haihuwa bane, ba ma haka ba, wannan fa yar uwarki ma cece, ya kamata ko don wannan matsayin da kuke daya ki taimaka mata". Kallo uku ahu tayi mata, kafin ta gyara zaman gilashin fuskarta. "karki jefe ni da wasu kalamai munana, karki ga laifi ne akan wannan lamarin, ke kanki sani, duk wata mace mai ciki in dai ta zo haihuwa sai an bukaci katin zuwa awonta, kafin a dubata...". "wannan ba hujja mace malama". Mai Napep ya katse mata maganar da take yi, cikin zafin rai ya dora da cewa. "wannan maganganun da kike duk na banza wallahi, na lura ba ki da imani sam ke da wasu likitocin da kuke aiki, in har haka likitoci suke sam ba su yi ba a duniyar nan ko daya, ke ba zan musu kudin goro ba, dama komai na duniya akwai na gari akwai kuma bara gurbi, to ke ki na sahun bara gurbin wallahi". Yanayin da yake maganar cikin zafin rai kamar zai rufeta da duka, ya fadar mata da gaba, nan ta shiga duban su daya bayan daya har takai ga Malam Bello, wanda idanuwansa gabadaya sun gama rinewa kamar wanda aka watsawa barkonon tsohuwa girgiza kai tayi gami da cewa daga dakin, adaidai lokacin Habeeba ta saki wani nishi wanda ya sanya gabadayansu suka dire akanta, numfashi take saki cikin wani irin wahalallan yanayi mai dauke da rashin hayyaci, idanuwanta a rufe amma hakan bai hana hawaye zubowa ba, Malam Bello ya isa gareta, gami da riko hannunta ya na ambatar sunanta, cikin murya mai taushi da tausayi, girgiza kai ya ga tana yi hawaye na kara balle mata, bakin sa na rawa ya shiga kokarin yin magana amma kamar wanda ka daurewa harshe maganar taki fitowa, ya shiga goge mata gumi dake ta faman tsantsafo mata a goshi. a daidai wannan lokaci wani dirkeken mutum, wanda da kallaeshi za ka gane babban likitane, yana gaba Nurse na biye dashi har ya iso inda Habeeba ke kwance, dubanta yayi sosai kafin ya komar da kallonsa izuwa wajan Malam Bello, wanda yake ta famam ajiyar zuciya. "mai ya sa haka, mai yasa har kuka bari hakan ta kasance a gareta?". ya fadi cikin murya mai nuna bacin rai. Girgiza kai ya shiga yi cikin rashin abin cewa, likita ya sake dubanta. "ina katin ta wanda take zuwa ganin likita da awo dashi". Nan ma girgiza kai yayi, alamun babu kenan. Da sauri likitan ya dube shi cikin alamun zaro idanu waje, da madaukakin mamaki da kuma haushi. "hakan da kuka yi sam bai da ce ba, ka ga yanzu kun haifar mata da matsala, domin duk wanda ya kalleta ya san tana cikin halin wahala, ya kamata kuke lura mace mai ciki tana bukatar taimako da kulawa da tattali, tun daga lokacin da ta samu ciki ya kamata ace tana zuwa Asibiti, a ko wani bayan sati uku tana ganin likita, hakan ne zai bata damar sanin halin da take ciki da abin dake cikin ta. kar ku ga laifin abinda wasu likitoci ke yi na rashin bada kulawa ga mai ciki, hakan na faruwa ne ta dalilin mai ciki da kum mijinta...". "kayi hakuri likita don Allah, a bar zancen nan, ya kamata ace ku san abin yi akan wannan baiwar Allah, domin tana cikin hali mara dadi". Daya daga cikin matan dake wajan ta fadi, cikin yanayi na rauni. Murmushi likita yayi ,kafin ya shiga duban Habeeba, daga karshe ya umarce da su dauke ta domin zuwa dakin haihuwa, yana tsammanin haihuwar ce ta zo, cikin hanzari kuwa sukayi hakan. likitin ya kira Nurse uku, sukayi masa jagora domin kula da Habeeba, Malam Bello da sauran matan suka koma harabar Asibitin suka yi cirko-cirko, mai Napep nan yayi wa Malam Bello Sallama tare da fatan samun lafiya ga Habeeba ya tafi. ba tare da ya amshi ko sisin sa ba. Sai da suka shafe mintina talatin, amma har zuwa lokacin ba alamun haihuwar za ta yiwu, tun likitar na tsammani har ya fara yanke tsammani. iya kokarin sa yayi amma bai kai ga ci ba, ga dai kan jariri a waje amma fitowarsa ya gagara, duk wani taimako yayi amma ina domin gabadaya jaririn ya cije ba alamun zai fito, dalilin kin buduwar kwankwason ta, yaki budewa balle jaririn ya fito, iya wahala Habeeba ta gamu da ita, shi kan sa jaririn wahala ta sheshi, ganin wanki hula na kokarin kai su dare, nan likiti ya fito ya ja hannun malam Bello, zuwa Office din sa, yayi masa bayani, ba karamar kaduwa yayi ba, nan likita yace in ya yarje ayi mata aiki, domin shine kadai mafita agareta, da ma jaririn domin kar azo ayi BIYU BABU. Shiru yayi yana tunanin lamarin, ba wai aikin ne ba ya so ayi mata ba, a,a kudin aikin in da zai samo su, ita ce matsalar. domin kuwa a yanzu halin da ake ciki ko dubu biyu na sa takan sa ba shi da ita, balle wasu makudan kuɗaɗe da yake tsammanin za a nema a gareshi, numfashi ya ajje ya dubi likita wanda ya gama karantar halin da Malam Bello ya ke ciki. "Likita ba wai ba zan iya sa hannu ba ne, a,a abin neman ne babu...". Hannu likita ya daga masa, yana kokarin yin magana. kamar daga sama Nurse ta fado cikin office ta dubi likita. "Sir ina tunani za ta iya haihuwa da kanta...". Tun kafin ta dire, ya miki zumbur cikin hanzari, ya fice daga office din .Nurse ta biyo shi a baya tare da Malam Bello. yana shiga dakin ya tadda sauran Nurse din akanta, yanayin da ya ganta da irin nishin da take saki ya kara sanya jin tausayinta, da sauri ya isa gareta, izuwa wannan lokacin kafaɗar jaririn ta yo waje, hakan ya tabbatar masa za ta iya haihuwar da kanta, a hankali ya fara kokarin janyo jaririn a hankali a hankali yake bi har ya zo matakin tsakiya, wato saitin cikin jaririn. a lokacin ta yi wani nishi mai dauke da wata hargitsattsiyar kara, wacce ta amsa kuwa gabadaya dakin. a sa'ilin da shi kuma jaririn ya fado duniya gabadaya. zubewa tayi daga kan gwuiwowinta numfashin ta na fita, cikin wani irin yanayi... [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA BABI NA UKU Kuri likita yayi mata da idanu gabadaya hankalin sa da guntuwar natsuwar sa tana kan ta hannusa kuma yana mikawa nurses jaririn bayan ya yanke masa cibiya. Abubuwa ne suka shiga yi masa dirkar mikiya a kwakwalwa zuciyarsa na ta tunano masa wasu abubuwa da baya fatan ace sun faru da wannan baiwar Allah ajiyar numfashi yayi gami da saurin duban Nurses da suma hankalinsu na kanta ganin halin da take ciki na rai kwakwai mutu kwakwai. "maza kuje ku gyara jaririn sannan kuma ku dauko gado domin daukarta don na lura tayi matukar gajiya da galabaita". Abin da likiti ya kokarta furtawa kenan cikin rashin tsammanin samun karfin daga laɓɓa har ya yi furuci gyaɗa kai yake yi yana gauraya kwayar idanuwansa cikin gurbin su laɓɓansa dake cikin bakin sa sai faman cizon su yake fuskarsa na kara bayyanar da rashin armashi da natsuwa. Mikewa yayi cikin rashin kumaji duk wani azancin sa yana jin yarda yake kokarin kufce masa daurewa kawai yake yi yana yaki da batun da kwakwalwarsa da zuciyarsa suke ta sanar dashi ba zai so haka ba, ba ya faman haka ta kasance gyaɗa kai ya cigaba da yi kamar yana magana da wani ya ma rasa abin da ya dace yayi tunaninsa gabadaya ya wargaje sai akan abu daya wanda yake tsammmanin ba ɗa mai ido zai haifo ba. Dawowar nurses ne ya dawo dashi daga duniyar fargaba da tsunduma ya shiga jan numfashi a hankali mai dauke da kayan tashin hankali Ya dube su su duka yana mai kaɗa idanu yana mai yi musu nuni da ita nan suka shiga gyara mata jiki tamkar gawa haka suke sarrafa har suka kammala sannan suka daurata zaman gadon gami da gungurawa suka fice daga cikin dakin yana mai bin su da kallo numfashi ya ajje gami da jingina da jikin bango har zuwa lokacin zuciyarsa sai kokarin gasgata masa lamarin take wanda shi sam ba ya fatan hakan wuyar rigarsa ya gyara gami da jan jiki ya fice daga cikin dakin xan gefe ya hango Malam Bello tallabe da haba sai faman mazurai yake yi cikin yanayi na rashin kwanciyar hankali kallo sosai likita ke bin sa da shi zuciyarsa na dauko tausayinsa tana jingina masa ta kowani bangare na sassan jikinsa sannu a hankali ya fara kokarin jan jiki ya isa gareshi amma sam bai san ya iso ba har sai da ya daf kafadarsa wata irin zabura yayi mai dauke da ajje wani gwauron numfashi idanuwansa fes kan likiti jikinsa yana rawa ya riko hannunsa. "don Allah in har zaka yi furuci kayi wanda ba zai tafi da imanin zuciyata ba na rokeka". yanayin da yake sakin furucin da kyar yasan ya jikin likita kara sanyi ya shiga gyada masa kai. "ta haihu...". shima ya fadi dakyar kamar wanda akayi wa dole idanuwansa na kan Malam Bello kamar yarda shi ma ya ke kallonsa zare hannunsa yayi saboda wani irin bugu da yaji ya kawo masa ziyara zuciya ya dubi Malam Bello. "ina zuwa zan maka magana in an kammala gyara mata jiki sai ka zo ka ganta da baby ko". ya karashe cikin sakin murmushin yaƙe bai jira amsawar Malam Bello ba ya ja jiki da sauri ya nufi dakin hutu da aka kai Habeeba ya tura ya shiga har yanzu dai jiya-i-yau da sauri ya isa gareta yana duban nurses da sukayi carko-carko da alamun yanayin da suka ganta ya tafi da yar guntuwar jarumtarta su hannunta ya kamo bayan ya dan rankwafa zuwa gareta hannun ya shiga juyawa yana mai kai dayan hannun nasa izuwa wuyanta yana taba alamun nemon motsin numfashi cak! ya tsaya kamar wanda aka cewa in yayi kwankwarar motsi ba zai ji sautin saukar numfashin nata ba gyada kai yake yi cikin raguwar faduwar gaba jin saitin kirjinta yana harbawa alamun da rai a jikinta har zuwa wannan lokaci ajje numfashi yayi mai karfi kafin ya miki ya shiga binciken ta sosai tsayin wani lokaci bayan ya kammala ya umurci Nurses akan su dauko masa kayan karin jini cikin sauri suka fice gami da daukowa ruwa ya fara sak mata gami da yin wasu allurai a cikin ruwan sannan ya juya inda ya juyo jaririn na kuka inda aka kwantar dashi kallonsa yayi sosai ɗa namiji ne fari tas dashi kyankyawa mai kama da uwarsa. Barin wajan yayi, ya yi hanyar fita waje. A bakin kofa ya tadda Malam Bello tsaye ya na jiran fitowarsu, da hanzari ya isa gareshi dauke da fuskar murna sai faman tallar hakoransa yake yi kamar wanda aka baiwa sabuwar amarya amma in ka lura sosai zaka tabbatar da murmushin na yaƙe ne cikin kokarin dauko jarumta ya dorawa kansa ya isa gareshi shima da ya hango shi cikin hanzari ya baza masa idanu yana takowa a hankali kamar kazar da kwai ya fashe mata a ciki lura da yayi fuskar likita da murmushi sai faduwar gabarda take wa kirjinsa bugun kato ta fara saurarawa yashiga ajje numfashihar suka iso ga juna suna shakar numfashi Malam Bello ya sake ajje numfashi yana mai gyara zaman hular kansa ya shiga jiki na ɓari ya dubeshi. "likita ka ja min rai wallahi, don Allah sanar dani halin da ake ciki, ko na samu raguwar bugun katon da zuciyata ke yi". ya fadi yana kara kusanto shi kamar zai shige jikinsa idanuwansa fes akan sa. zuciyar likita tayi matukar cilla cikin wani hali na ta rarrabi na rashin tabbas akan lamarin da yaji duniyar tunaninsa na shawagi dashi a ciki ya rasa mazaunan hankalisa sun ka sa zaman kalau ya tabbata zuciyarsa bata yi masa adalci ba in har ta dauko mata banzan tunanin nan wanda in har ya gasgatashi komai zai iya faruwa wani yake ya kinkimo ya daurawa fuskarsa tare da dafa kafadar Malam Bello. "ta haihu lafiya an samu ɗa namiji ina tayaka murna...". Sautin ihun da ya dauki cikin asibitin gabadaya shi ya daskarar da duk wani motsi na mutanan cikinsa ya tafi da furucin su likita da yayi mutuwar tsaye idanuwansa fes akan na malam Bello wanda shi ma kallo daya zakayi masa ka tabbatar zuciyarsa ta shiga halin tsoro matuka da ihun da ya karaɗe cikin asibitin da saurilikita ya juya ya yi dakin da Habeeba take ba wai don ya na da yakinin daga dakin ihun ya fito ba kawai zuciyarsa ce ta ja linzamin hankalinsa izuwa dakin ilai kuwa yana kokarin shiga suka ci karo da Nurses cikin yanayi na firgici da razana bakin ta na rawa ta shiga nuna masa cikin dakin da hannuamma sam ta kasa kokarin fadin wani abu da zai zarewa likita yarjewa kansa Habeeba ce tayi wannan ihun da hanzari ya fada cikin dakin malam Bello dake bin su a baya shima a daidai lokacin ya fado ciki. Zaune take taɗe jikinta waje daya hannayenta cikin kunnuwanta sai faman zabga ihu take yi jikin ta na faman kyarma kamar wacce akayi wa tsinannan duka. kan ta su kayi gabadayan su malam Bello yana isa ya zauna kusa da ita yana mai kokarin janye hannayenta daga kunnuwanta yana mai dago habatar idanuwanta ya gani sun kaɗa sunyi jajir sai hawaye da suke kwaranyowa gabansa yayi mugun faduwa ganin irin halinda take ciki na rashin hayyaci juya wa yayi da sauri ya dubi likita bakin sa na rawa shima likitan idanuwansa na kanta domin abin da yake tsoro ne ya faru domin kuma ko tantama ba yayi ta samu matsala akan ta gau da kai yayi daga kallon da Malam Bello ke yi masa ya isa kusa da Habeeba ya kira sunanta amma ba ta amsa ba domin bata san ma yanayi ba sam! duban Malam Bello yayi cikin murya mai dauke da rauni. "yi mata magana sanar da ita kai wanene". da mamaki ya shiga duban likita jin abin da ya ce dashi gabadaya ya ji kansa na juyawa wasu lamura na tashin hankali yaji sun kawo masa hari ba shi ya mike yana nuna likita da hannu. "ban gane zancen naka ba sam, taimaka kayi mani fashin baki, ta ya ya zaka ce na sanar da ita wanene ni, bayan nasan kuma mun san junanmu ba bakin fuskoki bane mu a tsakani don Allah likita ka fahimtar dani abin dake faruwa". Ya karashe yana mutsuttsuka wuyar rigarsa yana mai cizon laɓɓansa ransa sai faman daci da fargaba yake yi domin yarda ya lura da canjin likita ya tabbata akwai matsala a tsakanin rayuwa matarsa kukan da jaririn ya saki ne ya sanya shi saurin juya inda ya juyo kukan da sauri ya kara kusa da gadon da jaririn yake kwance sai faman wuntsil-wuntsil yake yi da kafafuwansa hannunsa cikin bakinsa da alamu yinwa yake ji bai san halin da duniyar ta sa ta zo masa dashi ba hannu ya saka yadauki jaririn wanda yake nannaɗe ido ya zuba sa sosai yana ƙare masa kallo zuciyaraa da kasar ruhinsa sai hasaso masa abubuwa suke yi ma bambanta so da kaunar ɗan nasa yaji sun tsargar masa a jiki da jinin dake gudana ta ko ina a gareshi. Hannu ya saka ya dauko jaririn kafin ya juya na kallon likitan. "kace mani wani abu don Allah ko na samu saukin kunar rai da na zucci". Idanuwa duk suka zuba masa ganin yarda yake magana cikin yanayi na wahalallan yanayi da rashin hayyaci. Likita ya shiga gyaɗa kai kamar kadangare kafin ya nisa. "ban san ya zan fara yi maka bayani ba amma dai zan ce maka ka yarda da ƙaddara ko wacce iri ce ta fado rayuwarka". "ƘADDARA". malam Bello ya furta kalmar cikin jan numfashi da fada ruɗani. Ya shiga nazarin kalmar shi dai ana sa tunani ya san abin da ake nufi da ƙaddara akwai kaddara mai kayan farin ciki akwai kuma akasinta shi dai a yanzu ya san kaddarar sa ba mai dadi ba ce. "likita kayi min bayani yarda zan fahimta zuciya ta na cikin bala'i". Ya fadi yana mai dauke gumin dake karyo masa kamar wanda ya fito daga surace hannunsa daya kuma jariri ne sai faman wuntsil-wuntsil yake yi yana tsotsar hannunsa alamun yunwa yake ji. "...Uhmm nace ya kamata ka nemo wacce zata kula da ita na dan lokaci kafin komai ya zama daidai". Likita ne ya fadi haka cikin rashin abin cewa. Kallon sa yake yi, kallo na tuhuma mai cike da son karin bayani akan komai, kallon sa yake yi na rashin yarda da yanayin da ya gan sa a ciki, kallon sa yake yi cikin bugun zuci da ruhi. idanuwansa ya shiga juyawa akan ko wani dayan su cikin yanayi na kara tsoro da fargaba gani yake yi kamar Habeeba mutuwa zatayi in da a kwance take zai iya cewa mutuwa tayi amma suke boye masa amma zaune take cikin wani irin yanayi wanda shi kan sa bai san a matsayar da zai ajje shi ba. Nisawa yayi gami da juyawa ya ajje jaririn kafin ya dubi likita. "bana tsammani zuciyata zata yarda da kai da sauran ma'aikatan ka, na lura kana boye min wani abu da yake boye, likita in kayi min haka ba ka yi mani adalci ba sam, kuma ba zan yafe maka ba". Magana yake yi wanda da ka kalle shi zaka tabbatar ba isasshen hayyaci a gareshi. Gyaɗa kai likita yake yi tausayin sa na kara narkar masa da zuciya cikin jan jiki ya isa gareshi ya dafa kafadar sa. "kayi hakuri kayi abin da nace". "bani da wannan natsuwar, ka taimaka". Idanu ya zuba masa sosai kamar wanda ya ga bakuwar fuska, bai san mai zai ce masa, ko ma ya samu abin cewa ba tabbacin zai iya kamar sa domin yasa dole abin da yake faruwa ya fado cikin abin da zai ce dashi. "kai nake jira likita kace min ta haihu kayan farinciki kenan amma kuma naji kana kokarin dauko min kayan da za su ruɗani cikin wannan lokaci, na lura akwai abin dake kokarin faruwa, koma nace ya faru amma ka ki ka sanar dani". zuciyarsa ce ta fada masa da ya kawai fada masa domin ta san koman daren dadewa dole abin da ke boye ya fito fili. Kallon Habeeba yayi wacce take takure waje daya kamar wacce ake kokarin cire mata wani abu daga jiki ta hada gwuiwa da kai sai sakin numfashi take yi kadan-kadai "Uhmm...". Sai kuma yayi shiru yana duban Malam Bello ya ma rasa da mai zai fara wani tunani ya fado masa zuciya lokaci guda da sauri ya dubi Nurses ya ba su Umarni cikin yanayi na amfani da ido a take suka gane abin da yake nufi da sauri suka fice daga cikin dakin. Malam Bello ya dubi Likita izuwa lokaci. Zargi da kokwanto akan sa ya fara samun mazauni sosai a zuciyarsa. "ina ga kawai gida zaka ku tafi da ita tunda ta haihu lafiya...sai dai in ko wata matsalar ta faru sai ka dawo da ita". Tunda ya fara magana Malam Bello ke yi masa wani irin kallo mai dauke da TUHUMA hakan ya sanya jikin sa sanyi domin ya lura sam bai abince da batun sa ba. Juyawa yayi da sauri ya fice daga cikin dakin ya barshi tsaye shanye da baki hannunsa ruke da ɗan jaririn da izuwa lokacin ya fara kuka mai sauti sosai. kallon Habeeba yayi har yanzu dai tana nan yarda take isa yayi gareta yana mai zama kusa da ita. "HABEEBA". ya kira sunanta cikin wata irin murya mai taushi. ba ta dago ba, balle ya saka ran zata dago idanuwanta har ta sauke su akan sa, ko motsi ba ta yi ba, illa sautin ajje numfashi da take yi. Sake kiran sunan nata yayi a karo na biyu nan ma bata dago ba balle kuma ya sa ran zatayi magana. Tsayin lokaci suka dauka cikin haka shikuwa jaririn sai zunduma ihu yake yi sai faman jijjigashi yake yi amma ba alamun zai daina kukan mikewa yayi tsaye yana zarya cikin dakin yana duban Habeeba gabansa na kara tsinkewa da lamarin nata musamman da ya ga duk kukan da jaririn yake yi ko motsi bata yi ba. Nurses ne suka shigo ba tare da sunyi masa magana ba suka kama hannun Habeeba suka fice da ita yana mai bin su da kallo kamar wani sauna abubuwa da yawa sun daure masa kai ya rasa a ciki wanne ya kamata ace yayi tunani akai da ya dauko zaren tufka tunanin nasa sai ya warware haka ya cigaba da zarya domin rashin abin yi kusan mintina biyar yana cikin wannan yanayi sai ga likita ya shigo yana duban sa. "An kammala komai ka zo ku tafi don Allah ka kula da ita sosai domin ba karfin jiki gareta ba haihuwar ta bata wahala matuka kai kan ka sheda ne don haka a kula mun yi mata duk wani bincike da ya kamata, zamu hadaka da ma'aikaciyarmu daya domin akwai abin da muke bukata ta kula dashi". tunda ya fara magana yake gyaɗa kai cikin amincewa amma ba har zuci ba kawai rashin abin yi yayi ya bige da amsa maganar da ba yarda yayi da ita ba. Duk halin da yake ciki Likita na lura da shi haka ya ja shi suka fice daga daki har zuwa inda motar da aka saka Habeeba tana zaune a takure kallo kawai ya bita da shi yana gyaɗa kai cikin rashin taka maimai in da zai ajje tunanin da yake yi akan ta. gaban motar ya shiga rungume da jaririn can baya kuma Habeeba ce da Nurses zaune gefen ta sai direban da zai ja su. Sosai da sosai likita ke tausayin su a zuciyarsa sai faman gyaɗa kai yake yi har ya ga tashin su suka bar harabar asibitin... [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA. BABI NA HUDU Kamar wacce aka watso haka ta fado cikin gidan, kallo daya za kayi mata kayi tunani rainon dawanau ce gabadaya yana yin jikinta ba shi da maraba da wacce aka durbuɗe cikin jar kasa ana cakudawa har sai da aka ga ta canza launi aka sake ta. "Ahayye Yaro Ahayye Yaro, A ƙyawu wata tafi wata a taku koni nafi". Waƙar da take ta faman yi kenan da tayi tafiya daya biyu za ta tsaya tana girgiza kugu gami da tafa hannu a haka har ta isa kofar daya daga cikin dakunan gidan ba sallama ta bankaɗe labule ta faɗa. Goggo Marka dake zaune tana faman ƙadin zare zumbur tayi tana shirin arcewa don ba karamar tsoro taji ba wani irin kallo ta watsa mata bayan ta ga wacece. "ke kam an yi 'yar wofi wallahi ai wannan sai ki tsinkar min da gaba". turo baki tayi gama tana mai galla mata harara. "Uhmm nikam Goggo ki daina ce mani 'yar wofi". "ke dalla jaye ki bani waje yar banzar 'ya mara hankali". "nikam ba 'yar banza bace". ta fadi tana mai yatsine fuska. Juyawa tayi zata fice daga cikin dakin da sauri Goggo Marka ta dakatar da ita ta hanyar cewa, "haba 'yar gidana ba ma haka dake, ina kuma zaki je?". ko sauraron ta bata yi ba ta kara azama wajan ficewa daga cikin dakin da sauri ta mike ta riko hannunsa cikin karya murya. "haba hafsatutuna yar gidan Mati da Abulle jikanyar Goggo Marka yar gaban goshin Danliti kar kiyi fushi mana". Da alamun kirarin da akayi mata ya yi mata dadi shagwaɓe fuska tayi. "Nikam in har kina zagina zan bar zuwan gidan ki ke kenan kullum zagin mutum". "yi hakuri na daina, yo ai kece da turawa mutum haushi ba ki iya abin hankali ba amma dai yi hakuri zo mu zauna in ji abin da ke faruwa". ba musu ta koma cikin dakin ta zauna ta shiga jayo kayan kaɗin Goggo Marka tana kokarin batawa da sauri ta buge mata hannu. "nifa tsiya ta dake kenan ba kya gani ki kyale sai kin taba". harara ta galla mata. "kwarankwatsi zan daina zuwa gidan ki ke abu kadan sai ki daki mutum ko ki zage shi". Hafsatu jikan Goggo Marka ce ba ta ji sosai da sosai rashin jinta ya wuce inda kake tsammani kullum cikin kawo wa uwarta korafi ake yi duka kuwa kullum cikin shan sa take amma ba abin da yake sauya zani ba wanda bai santa ba cikin kauyen nan iyaye da yawa ba sa son suka ga 'ya'yansu da ita domin rashin jin ta da kangarewrta sau da dama in tayi laifi bata zaman gida domin tasan halin uwarta jibgarta take yi kamar Allah ne ya aiko ta shiyasa da tayi laifi sai ta kwaso jiki tayo gidan Goggi Marka wacce ita ce bata ganin laifinta ko fada ta tsokano in dai ta zo wajan ta sai dai ta balbale wanda ta tona da masifa da zagi a wajan Goggo Marka ta samu daurin gindi take tsula tsiyar ta yarda take so sai dai kuma wani abu dake faruwa tsakaninsu duk son da Goggo Marka take yi mata bai hana a dinga jin kan su ba kullum in har ta zo gidan ba ta barin sa ba suyi fada ba Goggo Marka bata da hakuri sam kamar zawo ita kuma Hafsatu ba ta ji kamar 'yar Allah bani. Mikewa Hafsatu tayi tana kokarin ficewa daga cikin dakin da sauri ta ce da ita. "ina kuma za ki je?". Cikin rashin baiwa maganarta muhimmanci tace. "aƙwai zafi yasin dakin ki sosai ba zan iya zama ba, bari na zauna waje". ba ta tsaya jin abin da zata ce da ita ba, ta bankaɗe labulan ta fice nan kofar dakin ta samu kujera yar tsugunno ta zauna ta shiga sakin yan waƙoƙin ta na shirme a zaunan ma rawa take yi. Mariya dake kunshe cikin daki cikin wani irin yanayi na rashin tsammani komai na rayuwa domin ta gama yankewa kanta ta rabu da uwarta kenan tunanin ta sai wansafo mata abin da yake wakana da uwarta yake yi aceqar ai ta jima da matuwa gawarta kawai za a kawo gida lokaci-lokaci hawaye da suka zama abokan zamanta a wannan lokaci sai faman zubowa suke amma ko ta kan su ba ta bi don ta tabbata ko dauke su tayi ba abin da zai ragu daga tashin hankali da take ciki saboda komai na duniyarta ya kwance mata. juyi take yi lokaci lokaci abubuqa sai faman kara yawa suke na tunanin zuci masu tayar hankali. kamar wacce aka tsikara haka ta mike zumbur cikin taimakon jarumtar zuci jiki kuma a sake ta miki sai faman tangaɗi take yi kamar wacce ta baje aka idanuwanta sun kaɗa sun yi jajir kamar wacce akayi wa surace da barkonon tsohuwa sannu a hankali ta fara jan kafar ta har zuwa kofar dakin ta dage labulan ta fito ba ta lura da Hafsatu dake zaune ba can gefe guda ta shiga kokarin yin waje motsinta ne ya sanya Hafsatu dagowa daga abin da take yi ganin Mariya ya sanyata jan jaki domin ba shiri suke yi ba sam! Jininsu bai haduba. sarai ta ji tsakin da aka ja amma ba ta tsaya daga tafiyar da take yi ba domin tashin hankalin da take ciki ya zarce ta tsaya neman ba'asi ko da bugun ta kuwa akayi a daidai soron gidan su ta tsinkayi tsayuwar Napep cikin wani irin karfi da bata san tana dashi ba ta kwasa yi waje a guje adaidai lokacin Mai Napep din ya tsaya turus! tayi ta tsaya ba tare da ta isa wajan da suke ba idanuwanta kuriii kan na mahaifiyarta abubuwa ne suka shiga yi mata shawagi akai gani take kamar ba gaske ba gani take kamar mafarki ne yake kokarin yaudararta. ba ta san lokacin da Malam bello ya fito ba har ya biya mai Napep kudin sa Ya dubi Nurses. "zaki kamo ta ku fito ko sai na taimaka muku". "barshi kawai shiga da jaririn cikin gida tukunna". Habeeba ya kalla har yanzu tana nan yarda take ba abun abin da ya canza domin tunda suka taho maganar duniya yayi mata amma ko tari bai ji tayi ba girgiza kai yayi gami da daukar hanyar cikin gidan Mariya da tajima cikin tunani ba ta san lokacin da ya iso ba ya dafa kafaɗarta firgigit tayi tana mai baza idanuwa kamar wacce zata arce kallon mahaifinta tayi da abin da ke hannunsa kanta taji yana juyawa gani takeyi kamar ba gaske gani take yi lamarin kamar ba faruwa yayi sai da taji ya ambaci sunanta tare da girgizata sannan ta tabbatar da abin da take zargi ta shiga duban jaririn ta na kallon mahaifinta murmudhi take ajjewa wanda bata san ya akayi ta samu damar yin sa ga ruwan hawaye sai kwaranyo mata suke. Shima murmushin yayi mata wanda shi da ka kalle nashi bai kai zuci ba iyakarsa fatar baki. "jeki ga Umman taki can". ba ta tsaya tanka masa ba tayi hanzarin barin wajansa ta nufi Napep in da ta hangi Nurse na kokarin fito da ita shi kuma ya fada cikin gidan. tun kafin ta isa gabanta ya yi wani irin bugu lokaci guda taji wani irin yanayi ya ziyarce ta zuciyarta na sanar da ita an samu matsala, matsala babba. da sauri ta isa gaban Nurse tana kallon ta cikin wani irin yanayi kamar mai son karin bayani kallon Ummanta tayi wacce ta zama tamkar rakumi da akala ba wani kuzari sam! a gareta sai yarda Nurse tayi da ita. "NA SHIGA UKU!". Mariya ta fadi gami da riko Ummanta kallonta sosai Nurse tai jin abin da ta fadi girigaza kai tyi cikin yanayi na tausayi a haka suka rungumi Umma sukayi cikin gida da ita wacce a wannan lokacin sam bata san a ina take ba duniya ce ko lahira haka suka isa cikin gidan a lokacin Malam Bello ya fito daga cikin dakin ya na musu nuni da dakin ta ciki suka shigar da ita Duk abin da ake yi Hafsatu tana nan zaune shanye da baki mamaki ne ya cika ta sosai ganin an shigo da Habeeba ya sanya ta saurin mikewa ta fada dakin Goggo Marka tana kiran ta. "Goggo zo ki ga Umman Mariya ta haihu". dubanta ta shiga yi da mamaki don ita sam ta mance da cewa Habeeba na nakuɗa har sun ta fi asibiti cikin hanzari ta mike tana duban Hafsatu cikin murya kasa-kasa. " wa ya ce miki ta haihu?". "yanzu naga sun shigo Malam rike da jinjiniya sai kuma wata mata ringome da Umman Mariya...". kuri tayi mata da idanu kamar mai son gano wani abu ita ma Hafsatun kallon ta tashiga yi cikin rashin abin yi kwankwasa kofar da akayi ne duk ya sanya su zabura Goggo Marka ta kalli kofarta jin muryar Malam Bello wani takaici ya turnuke ta ba shiri ta saki hannun Hafsatu kamar bata san abin da ke faruwa ba ta bankaɗe labulan tana kokarin tura ashar harara ta saki gami da jan guntun tsaki juyar da kan ta tayi cikin dakin cikin kunkuni. "gaskiya na shiha hakki wallahi, sai azo ai ta dannawa mutum sallama duk a firgita shi sai mutum yayu zaton mutuwa ce ta kawo farmaki". kasa-kasa tayi maganar amma sarai ya ji abin da take cewa ransa kuma ya sosi da maganar sai dai ya ki nuna hakan a fuska illa girgiza kai da yayi ya shiga kokarin yin magana. "kiyi hakuri Goggo, dama zuwa nayi na sanar dake Habeeba ta haih...". dariyar da Hafsatu ta saki ne ya sanya shi kasa karasa maganar sa domin bai yi zaton tana cikin dakin ba sam! ita ma Goggo Murmushi ta shiga saki, sai ka rantse na farinciki ne amma ina! ba haka bane duban sa tayi tun daga sama har kasa baki a kwaɓe. "Ikon Allah. ashe shiyasa na ga sai faman ɓarin jiki ka ke yi kamar wanda ya ga sabuwar Amarya". Gyaɗa kai ya shiga yi jin maganganun da take fadi ya tabbata ba har zuci ba kawai magana ce a fakaice take dankara masa. "Uhmm shi ne dama na zo na sanar dake...". bai dire ba, tayi saurin caɓewa. "Gaskiya kam!". Ta sauke guntuwar maganarta ta da dubansa tana mai sakar masa yaƙe. Shiru yayi yana ganin ikon Allah ran sa yayi matukar ɓaci musamman da ya lura dariyar da Hafsatu ke yi ta gayya ce da raini ita kuma Goggo ta hanashi sauke maganar da ya dauko nisawa yayi cikin haushi. "ba wani babba don Allah Goggi ki zo ki yi wani abu". "...haka fa na manta ashe watan tashin asuba na da wankar jego ya kama Hafsatu zo muje zaman mursu". ta fadi tana mai duban Hafsatu da take ta faman dariya Baki ciki iyaka Malam Bello ya shaka ji yake kamar ya fada cikin dakin ya shago Hafsatu ya jibga ko ya rage jin haushi amma ba damar haka don ya tabbata in har ya dake ta yau sai kowa ya ji a gari ga abin da yayi cikin rashin abin yi ya juya ya bar kofar dakin yana mai cizon laɓɓa. Isar sa cikin dakin ya tadda Nurse ta gyara ko ita da taimakon Mariya wacce natsuwarta rabi da kwata ba ta tare da ita tana ga Ummanta wacce take girke waje guda ba Uhmm ba uhm-uhmm. "ya kamata ace anyi wani abu izuwa wannan lokaci". Cikin rashin fahimta ya dubi Nurse yaka faman gyaɗa kai. "kamar me kenan?". ya fadi cikin raunin murya da rashin abin yi domin ya tabbata kayan bukata ake nema wanda ya tabbata ba shi da karfin yin su don ko wuka za a daura masa a makoshi baya magani kudin da za ace za ayi bukatu na azo a gani. "ya kamata ace izuwa yanzu an yiwa jiririn nan wanka itama.uwar kanta ta gyara jikin ta sannan kuma da abubuwan da za ta sanyawa cikinta". tun da ta dora zancenta yake faman binta da kallo yana gyaɗa kai cikin rashin abin yi ita kan ta Mariya kallon Nurse take yi domin abin da taji tana fadi to ta tabbata mahaifinta bai da wannan halin a yanzu haka ita sheda ce. kamar wacce aka tsikara ta mike tayi tsakar gida gindin murhu ita isa ta janyo guntayen itace da karare ta hada ta tada wuta ganin wutar ta kama ta mike da sauri ta dauko katuwar tukunya wacce rabon da ta ga wuta anjima daurayeta tayi taje ta daura kan murhun sannan ta shiga debo ruwa tana zubawa a hankali har ta cika ta fam ta sanya murfi ta rufe tana mai sakin ajiyar zuciya tana bin tukunyar da kallo abubuwa da yawa suna yi mata yawo cikin kwakwalwa tausayin iyayenta sai kara raunata ta yake yi ji take yi kamar ta fice domin samo abin bukata sai dai tana tunanin in ta fita ina zata je wajan wa zata ba ta sani ba ita ba namiji bane balle taje tayi aikin karfi domin sabun abin taimakawa iyaye ita 'ya mace ce kuma rauni gareta tana tsoron abin da zai kawo wa rayuwarta farmaki hawaye suka zubo mata hannu ta saka ta dauke su ta sake duban murhun wutar taga tana kokarin mutuwa da sauri ta durkushe tana hurawa da baki amma kamar kara kashe wutar take da sauri ta mike ta nemo wani yagalgalallan mahuci ta shiga fifitawa amma ina ba alamun wuta zata ci domin itacen yayi karanci sosai da sosai da sauru ta mike tayi waje yaye-yaye na ledoji da duk abin da ta san zai ci wuta tayo ta dawo ta shiga cusawa cikin murhun hayaki ya turnuke sosai nan da nan ta shiga tari idanuwanta suka kara rinewa zuwa jajaye suna zubda hawaye amma hakan bai hana ta kokarin tayar da wutar ba dakyar da gumin goshi wutar ta tashi bayan ta gama sharafin ta na hayaki ganin wuta ta kama ganga-ganga ya sanya yin zaman dirshan a wajan ta zabga tagumi tana kallon ikon Allah. Abubuwa take tunawa marasa dadi a rayuwar nan tun da ta fadi duniya ta tsinci iyayenta cikin wannan hali na rashin dadi tana bukatar fidda su daga cikin ƘANGIN RAYUWA sai dai ta rasa ta ina zata fara tana so ta samowa iyayenta YANCI amma ta rasa mai ya dace tayi ita yarinya ce amma kuma ta fara fuskantar matsalar rayuwa tun kafin ta kai haka in ana haddace matsalolin rayuwa ya kamata ace ta haddace su akana ta rasa tana ina zata fara kokarin tunkaran rayuwar nan domin samo wa iyayenta farin ciki [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA. BABI NA BIYAR "Sannu da kokari Mariya, Allah ya yi miki Albarka". Kamar daga sama ta jiyo sautin mahaifin nata ya na furta kalaman. da sauri ta shiga goge fuskarta tana faman ajje numfashi da kyar sai da tayi kokarin samowa kanta natsuwa sannan ta taso tana mai dubansa tana faman sakin yaƙe kamar wacce aka cewa in bata yi ba ranta za a dauka. "bari na fita naga yarda Allah zai yi damu". ya sake magantuwa idanuwansa fes akanta yana faman gyaɗa kai cikin yanayi na tauyasawa dukkan nin su. Sai da ta ajje numfashi mai rauni sannan ta nisa. "Allah ya kiyaye hanya". tana fadin haka ta shiga kokarin gyara wutar da ta hura domin ba ta son wata magana ta sake shiga tsakaninsu don kukanta a wuya yake in kuwa ta fiye magana komai zai iya faruwa. tana jin ta kusan sa har ya fice sannan ta saki ajiyar zuciya cikin ta cikin hali na sanyi ta ja shi domin kowa wajan mahaifiyarta tunanunnuka birjin cikin ranta. "Ahhhh ashe dai ba haihuwar guzuma akayi ba". Goggo Marka da ke tsaye tun dazu tana kare musu kallo da yatsine yatsinan fuska ta fadi haka lokacin da Mariya ke kokarin shiga daki. ba ta fahimci in da maganar ta dosa ba amma dai ta sakawa ranta cin fuska akayi mata gyaɗa kai kawai tayi ta kalleta na yan sakanni ta dauke kanta. "munahika ni kike kallo haka, mara kunya 'yar masu baki hali kalle ni da kyau ba dai zagina zaki yi ba don wallahi kika zage sai na dake ki dukan shan gishiri". da sauri ta fada cikin dakin don ba za iya jurar sauraron maganganun Goggo Marka ba ranta yayi matukar baci amma ba ta bari hakan yayi tasiri a fuskarta ba ta bar wa zuciyarta bakinta dauke da Sallama ta shiga dakin har yanzu Habeeba na nan yarda take can gefe kuma Nurses ringume da jariri dake ta faman rusar kuka tausayi da jiƙan duk ya gama jikin ta jingina tayi da bango ta na ajje numfashi idanuwanta kan mahaifiyarta abubuwa da yawa sunayi mata yawo akai amma ta rasa matsayar da za ta ajje tunaninta komai ya cakuɗe mata ya cinkushe mata ta kasa gane lamarin dake faruwa gabanta na faduwa sosai da sosai wanda ta hakikance akwai abin rashin natsuwa da yake shawagi cikin duniyarsu a yanzu. Duban ta take yi cikin rashim abin yi komai ya kwance mata laɓɓanta sai rawa suke yi alamun ta na son cewa wani abu amma ta kasa hakan hawaye sai ambaliya sukeyi zuciyarta na tukuki ba abin da ke shawagi a kanta illa rayuwar da take ganin tana tunkaro su wacce ta hakikance ba tabbanci kayan kwanciyar hankali acikin ta sai wani nufi na Allah. "gafaran ku dai masu jego". Muryar Goggo Marka ta karaɗe cikin dakin ba wanda ya dubeta tsakaninsu har ta gama shan sharafin ta sannan ta kaea tsakar dakin ta samu waje ta ajje kugunta tana mai duban Habeeba wacce take rakuɓe waje guda ta juya wajan Nurses dake ta faman jijjiga jaririn ta shiga yashe baki kamar gaske. "kai Masha Allah mikon min shi nagan shi". ta fadi tana mai turawa Nurses hannunta da ta bata jaririn ba musu ta mika mata ita ma tana faman yashe baki amma ba kai zuci ba tunani ne ya ke mata shawagi cikin kai akan Goggo Marka don bata yi tsammanin akwai wata mace a gidan ba tunaninta kawai su Mariya ne gyaɗa kai tayi gami da ajje tunanin gefe ta shiga kokarin mikewa tana mai duban Habeeba . "ni bari na koma bakin aiki tunda Baaba ta iso ko". ta fadi kamar mai son taji wata magana daga wajan Habeeba amma kamar a ajje dutse ko motsi sai Goggo Marka ce ta magantu. "Ahhh ya haka kuma na dauka kece mai zaman wanka". Cikin rashin fahimta Nurses ta shiga dubanta tana mai gyada kai tunaninta na dazu yana kokarin rugujewa akan Goggo Marka a tunaninta a gidan take zaune ashe ba haka bane barka ta zo yi gyaɗa kai ta sake yi sannan ta nisa. "A,a bani ba ce ni ma'aikaciyar asibiti ce". Kau da kai tayi ba tare da ta ce komai ba hakan da Nurse ta gani ya sanya ta isa kusa da Habeeba ta dafa kafadarta tana mai faman rausayar da kai tausayin ta sai kara tsargar mata yake tsayin mintina daya ta dauka sannan ta fara kokarin barin dakin bakin ta na yi musu fatan alheri. Bayan fitar Nurses Goggo Marka ta numfasa tana mai duban Habeeba domin zuciyarta sai faman tsegumi take mata akan yanayin da ta ganta a ciki. "na ganta cikin wani yanayi, me ke faruwa?". ta fadi tana mai kallon Mariya itama Mariyar ita take kallo cikin rashin abin cewa numfashi take ajje a hankali zuciyarta na faman harbawa kamar zata faso kirji ta fito. "dake fa nake kika yi mani banza, komai halin kurmantaka kuke ne yau ke da uwar taki". "...uhmm nima ban sani ba". Cikin ci da zuci ta furta haka tana faman jingine kanta da bangon dakin domin wani iri take ji duniyarta na yi mata sai shawagi kanta ke yi kamar wata waina cikin tadda. "kamar ya baki sani ba, nifa munafurci ne bana so kin ji ko". zuciyarta ta fara gajiya da lamarin Goggo Marka matuka. ji take yi muryarta nayi mata shawagi kamar zata tarwatsa mata kwanya cikin gajiya ta mike ta fice daga cikin dakin. Hakan da Goggo Marka ta gani ya sanya ta sakin tsaki gami da kwaɓa. "kin shiga uku da bakin halin ki". ta juya tana kallon Habeeba sosai da sosai take kallon ta tana son gano wani abu dake boye amma har tagama hangenta bata hango komai ba sai halin shiri da ta tsinta wanda ta rasa dalilinsa gyaɗa kai tayi gami da ajje jaririn kusa da Habeeba ta mike tana gyara daurin zaninta sai da ta karewa dakin kallo sannan ta fice. Mariya durkushe bakin murhu sai faman kokari take domin ganin ruwanda ta daura yayi zafi ko da bai tafasa ba ta san hakan yafi babu haka ta cigaba da gyara wutar har zuwa wani lokaci cikin Ikon Allah ruwan ya tausa sosai da sosai da sauri ta mike ta nufi dakin Goggo Marka gaban na bugu domin ta rigaya tasan da kyar ta samu komai a dadin rai a wajan ta. "ruwan ya tafasa". Dakyar ta furta hakan yanayi na rashin abin da za taji daga bakin Goggo Marka ilai kuwa magana ta caɓamata. "ni meye nawa a ciki, na dauka tun da kika iya dafa ruwan wanka jego na ai za ki iya wankan ma". maganar tayi mata kuna a rai amma ba nuna haka a zahiri ba sai ta shiga sakin murmushin yaƙe tana faman gyaɗa kai. "Uhmm Goggo kenan ba wai nayi gaban kaina ba ne kawai gani nayi hakan ma rage wani aiki ne...Uhmm ni dai rokona ki taimaka kiyi mata wankan". ta karashe cikin taushin murya mai cike da rarrashi. dubanta take yi sosai tana jin maganganun da take fadi ta juyar da kallon ta zuwa ga Hafsatu dake yashe bisa gado tana faman kallon su. "Amma dai...". "...Don Allah Goggo ki taimaka". Mariya tayi saurin tare ta tana mai hada hannayenta waje guda alamun roko idanuwanta tsaf! akan ta tana faman juya su kamar mai son fashewa da kuka. Ba wanda ya tsake tsinkawa a tsakaninsu tsayin mitina uku sannan Goggo Marka ta mike ta fice daga cikin dakin Mariya na biye da ita har wajan murhun suka isa ta duba ruwan sai faman tafsa yake yi ta juya ta dubi Mariya. "ni dai ba zan iya kwashe wannan tafasasshen ruwan ba tsakani har ga Allah don ba zan babbaka kaina ba". Gyaɗa kai Mariya tayi kafin tayi nishi. "bari in kwashe ni zan iya". Ta fadi cikin sanyin murya mai dauke da rawa sosai cikin karfin zuwa tayi wajan dakin Ummanta wani babban daro ta dauko wanda suke wanki dashi ta girke gindin murhun sannan ta bude tukunyar ta saka kofin da ta dauko ta shi ga kwashewa tana zubawa cikin dauro a hankali duk da ruwan na fallatsar mata a jiki amma hakan bai hana daurewa ba ta cigaba da abin da take yi sai da ta ga ta zuba sosai kwatankwancin yarda zata iya dauka sannan ta kinkima tayi hanyar bandakin su wandake zagaye da langa-langa ta ajje ta fito nan ta cigaba da kwashe ruwan a wani botiki tana kaiwa tana zubawa har sai da ta cika sannan ta tsagaita ta dubi Goggo Marka da ke tsaye tun dazu tana kallon abin da take yi. "na kwashe". "to yanzu ya za ayi kenan maganar ganyen wanka". Shiru Mariya tayi shaf ta mance da ganyen wanka da ake amfani dashi ko dayake ba abin mamaki bane rashin sanin haka gareta tun da ba sanin yarda ake yi tayi ba gyaɗa kai tayi cikin rashin abin yi. "Goggo kawai ayi mata ako da tsumma ne domin naji ana cewa nayi dashi tun da lokaci ya kure in za ayi mata na yamma sai a samo ganyen ko". Yatsine fuska tayi gami da kau da kai. "a ina kika taba jin anyi haka". Cikin sauri ta amsa mata. "a rediyo naji ana hira in mace ta haihu za ta iya wanka da tawul ba dole sai ganye ba". sakin baki tayi tana kallon ta cikin mamaki. "iyee Al'adun yahudawa kenan kike nufi za mu koma yi to ni dai ban san wannan falsafar taki ba ni dai A AL'ADATA ta hausa fulani da ganyen dogon yaro nasan ana wankan jego da wasu kuma dangin nau'ikan ganyayyaki domin akwai wani sirri da suke dauke dashi ni ban san wani ayi wankan jego da tsumma ko tawul ba...". "Don Allah Goggo ki taimaka". Mariya ta tare ta ganin tana kokarin cinye mata lokaci da suke dashi har ruwan wanka ya huce. "ni fa ba zaki sakani yin al'adun yahudu ba in har ba za a samo ganyen wanka ba to ba dani ba". tana gama fadin haka ta fara kokarin shigewa dakin ta da sauri Mariya ta shagabanta ta shigayi mata magiya da rantsuwar cewa in tayi mata wannan ba zata sake yi mata ba ba tare da ganye ba magiya sosai tayi mata sannan ta yarda. Mariya da kanta ta shiga dakinsu ta riko Ummanta domin ita Goggo ta ce sam ba zata taba jikinta ba haka da kyar da gumi ta fiddo ta daga cikin dakin sai faman nishi take yi domin gabadaya jikin Ummanta a sake yake ba abin da take yi sai yarda akayi da ita a haka har ta isa bandakin da ita kan wani dandamalin dutse dake tsakar bandakin da suke zama kan sa suna wanka. Ficewa tayi ta ba su waje ta koma can kofar dakin su ta zauna tare da zabga tagumi abubuwa sai mata shawagi suke mara dadi da armashi kamar wacce aka tsikara ta mike da sauri tayi cikin daki can in da jaririn ke kwance ta isa ta dauke shi gami da rungumeshi tana jin wani irin a zuciyarta tausayin sa take ji da yanayin da ya samu duniyar aciki ta tabbata yarda take rayuwa haka in shi ma ya tashi zai yi sai dai ba za ta so haka ba za ta so ace rayuwarsa ta fice daban da tata da take yi zata so ace bai fuskanci wani matsi ko ukuba ta rayuwa ba za ta so ace ya tashi cikin kwanciyar hankali da muradan farinciki cikin duniyarsa sai dai ba tabbacin haka zata kasance sai wani iko na Allah domin za ta iya cewa yanzu shigo ya ga rayuwar duniyarsa tun daga fadowarsa ya fara ganin rikicin duniya. Nisawa tayi gami da mai dashi ta kwantar ta fice daga cikin dakin wani karamin bahon wanka ta dauko ta zubo ruwan zafi ta sirka yarda take tunanin ba zai cutar dashi ba ko ya haifar mata da wata matsala dakin ta koma ta ajje ruwan sannan ta dauko shi zuciyar ta na faman buguwa tana tsoron abin da zai je ya dawo domin har kasar ruhinta tsoro ne fal ta yarda zatayi wa jariri wanka abin da bata san ya ake yi ba amma dai zata gwada ta gani domin ba zata iya barin kanin nata cikin wannan yanayi ba an haifeshi kusan a wanni amma ko ruwa vai gani ba. Tsunbulashi tayi cikin ruwan cikin yanayi na faduwar gaba aiko sai ya saki kuka lokaci guda da sauri ta zare shi jikin ta na faman kyarma ta shiga kallonsa idanuwansa bude sai faman lumshe su yake yi kamar mai jin barci sake saka shi tayi sai dai a wannan karon bai yi kukan ba illa ajiyar zuciya da yayi hakan da ta gani ya bata kwarin gwuiwa fara wanke masa jiki a hankali haka ta cigaba da yi ko sabulu babu sai da ta wanke masa jiki sosai da sosai har sai da taji ruwan ya fara sanyi sannan ta zare shi daga ciki cikin kayanta ta dauko wani zani mai dama-dama ta sakashi aciki ta nannade. Kiran ta taji Goggo Marka nayi da sauri ta mike rike da jinjirin ta yi waje tsaye ta tadda ita tayi jage jage da ruwa. "ki je ki fito da ita". nar-nar tayi da ido kamar mai son fashewa da kuka. "don Allah Goggo ki taimaka ki fito da ita wallahi ban zan iya ba dazu da kyar na samu na fito da ita kuma kin ga yaro ne a hannu na yanzu na gama masa wank...". ai ba ta dire zancen nata ba taji ta dauki sallallami tana tafa hannu kamar wacce ta ga mugun abu. "Mariya wanka fa kika ce ke yanzu har kin san yarda za kiyi wa jariri wanka". nan da nan jikin ta ya fara rawa hawaye suka fara sankoma mata dama abin da take gudu kenan abin da take tsoron faruwarsa kenan Allah yasa ba wani abu ne zai same shi ba Allah ba ganganci tayi ba cikin rawar baki ta fara magana. "Wallahi Allah ban yi...". cak! ta tsaya da zancen ta ganin Mahaifinta tsaye bakin kofa yana kallon ta nan da nan faduwar gabanta ya karu musamman da taga ya kafe da idanuwansa [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU BALA'I NA KAMALA MINNA. *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA SHIDA Da sauri ta dauke kanta daga barin kallonsa tana jin yarda sautin bugun kirjinta ke kara sauri cikin wani irin tashin hankali wanda sam ba tayi tsammani ba rintse idanu tayi iyakar karfin da taji a jikinta tana faman ambaton Allah komai nata take jin yana kwancewa komai take ji na duniyarta yana juya mata ji take kamar ba kan kafafunta take ba ji take kamar walagigi ake yi da ita jaririn da take daure a jikinta ji take kamar zai kwance ya fadi kasa da sauri cikin rashin abin yi ta kai hannunta zuwa saitin goyan ta rike sosai rikon da ko babban mutum akai wa shi sai yaji kamar za a dauke masa fata haka ta rike zanin goyan tana kara kankame jikinta waje daya ba abin da take jira sai hukuncin da take hangowa cikin idanun mahaifinta take zaton zai yanke akanta. A sukwane ya iso gareta ba tare da yayi magana ba ya kama kokarin kwance goyon nata ba karamar faduwa gabanta ya kara yi ba har zuwa lokacin idanunta a runtse suke kawai jira take yi taji duka ko ta ina don tuni ta yanke tsammani akan yarda ta ga mahaifinta ya nuna a fuskarsa na matsanancin bacin rai. "Mariya me ke faruwa ne?". Kamar daga sama ta juyo sautin muryar mahaifinta na fadin haka wata irin ajiyar zuciya ta saki gami da buɗe idanuwanta gabadaya ta sauke su akan sa tana mai faman gyada kai bakin ta na motsi. "Uhmm dama kawai shine...". Da sauri ya daga mata hannu lura da yayi yanayinta ya nuna a firgice take sai faman kucincina maganar ta ta take yi. "tambayarki nayi ba wai cewa nayi ki tsaya kwan gaba kwan baya ba". ya fadi yana mai karasa kwance goyon da tayi ya rungume yaron wanda a wannan lokaci barci ya fara tafiya dashi ya shiga dubansu ita da Goggo Marka wacce ta zuba musu ido tana nazarin inda za ta kullo zanar makircin ta. "Bello wai 'yar nan daga cewa bayi naje nayi wa uwarta wanka na fito nayi wa wannan yaron kawai ba da baya ashe ta kandami ruwan sanyi tayi daki ta zunduma shi a ciki ina daga bayani na ya saki kara hakan ya sanya ni fitowa a guje ko da na iso ya shaki ruwa har ya fara sheɗewa". Marka ta fadi cikin yanayi na dagaske ne abin da ta fadi har da dauko fuskar tausayi ta azawa kanta. Sosai yake duban Mariya yana karantar yanayin da take ciki yana kuma nazarin maganar Marka akanta yanayin da ya ga ta nuna alamun tsoro da firgici har da yar kwalla ya tabbatar masa ba tabbas a maganar amma saboda kar ya rikitowa kansa kwandon fitina sai ya dubi Mariya yana mai tsuke fuska. "me kikayi kenan mai yasa baki yi abin da ta ce miki ke yanzu har kin kai matakin da zata ce karkiyi kiyi sannan kuma ina ke ina yiwa jariri wanka sabon haihuwa kuma da ruwan sanyi ina kika taba ganinka haka...". caraf! Marka ta dauka. "yo hankali gareta ba gwanda ta nuna wa duniya uwarta ta haihuwa ba ga wadanda ba su taba zama a gwuiwa da sunan naƙuda ba". ta fadi ita ala dole gaskiya take fadi da neman bin da zai harzuka Bello ya jibgi Mariya. Riko hannunta yayi a tunzure ya jata kiiiii! Sukayi cikin dakin zuwa lokacin ta gama yarjewa kanta babanta dukanta zai yi nan da nan ta fara zubar hawaye tana faman bashi hakuri har suka isa cikin dakin ganin ba kowa aciki da sauri ya dubi Mariya. "ina Umman taki take?". "tana bandaki don Allah Baba..". tun kafin ta ajje maganar ta ta yayi wuf! ya ajje yaron ya fice daga cikin dakin da hanzari cikin kiɗima ya isa banɗakin tana yashe kamar yarda Marka ta barta ko motsi kirki ba tayi ta hade jikinta waje guda ta takure kamar wacce ake kokarin rabata da wani abu nata gabansa ne yayi wani irin mugun bugu har sai da yaji kamar kirjinsa zai buɗe da hanzari ya isa gareta ya na faman ajje numfashi mai karfi ya shiga ambaton sunanta amma ina! ba alamun zata motsa balle ya saka rai zata kalle shi jikinsa na ɓari ya shiga kokari gyara mata zanin da ke jikinta ya miƙar da ita tsaye ya haɗeta da jikinsa wani irin rawa yaji jikinta sosai da sosai. Gabadaya ya hadata da jikinsa wani irin tausayinta yaji yake tsaga duk wani sassan jikinsa lokaci guda yaji kwalla na kokarin zubo masa zuciyarsa sai faman zillo take yi tana faman hasasho masa abin da ba ya so ace ya tabbata domin in har hakan ya tabbata yana cikin matsala matuka gaya wanda sam ba zai samu murmushi ya cigaba da wanzuwa a fuskarsa ba. Cikin wannan yanayin na rashin tabbas da kwanciyar hankali ya isa da Habeeba cikin dakinta ya ajje Mariya dake can gefe sai faman kallo take bin su dashi gaɓadaya ta rasa gane kan wannan lamari zuciyarta sai wassafo mata abubuwa take wanda ba ta tsammanin na dadin rai ne niswa tayi wasu guntayen hawaye suka surnano mata ta sanya bayan hannunta ta dauke su gami da jan hanci. "Baba don Allah mu koma Asibiti". Abinda ta kokarta fadi kenan cikin muryarta mai rawa da kuka a cikinta. Ba tare da ya juyo ya dubeta ba ya cigaba da gyarawa Habeeba jikinta kamar ba zai yi magana ba domin bai san abin da zai ce bs ko da yayi niyyar yin magana a hankali yake sauke ajiyar zuciya bayan ya kammala gyara mata jiki ya kwantar da ita. juyowa yayi ya fuskanci Mariya sosai sannan ya dubi Yaron da ke kwance can gefe yana barci amma kuma hannunsa na cikin bakinda yana ta faman tsotsa kamar zai cinye shi da sauri ya kau da kai domin abubuwan tausayawa ne ya suka caki kirjinsa da sauri ya mai da duban sa ga Mariya. "nima ina tunanin haka Mariya domin kuwa wannan lamarin ya kamata ace an yi duba a kansa...". "wai don Allah ba za ka bar maganar asibitin nan bane Bello wai ina tunaninka ya tafi ne ya kamata ka zauna kayi amfani da MIZANIN HANKALI wajan nazarin wannan lamarin kai yanzu ba abin ka gujewa komawa asibiti bane ka duba ta kalau kuka dauki Habeeba zuwa Asibiti amma ka dubi yarsa ta ko tunda kuka dawo ko tarin ta ban ji ba balle na saka ran naji tana cewa wani abu kai ba abin ka tsorata bane da komawa asibiti in har ka na biyewa Maganar Mariya to tabbas zaka kashe matarka da kan ka domin ita yarinya ce ba ta san abin da ya dace da wanda bai dace ba kawai in haukar ta ta yanko mata zance haka zata faɗeshi ba tare da ta duba shi ba". "Amma Goggo...". Da sauri ta daga masa hannu alamar dakatarwa sa'anan ta daura da cewa cikin yanayi na bacin rai. "Shawara na baka in har ka ga za ka iya nikam ka ga tafiya ta". tana gama fadin haka ta fice daga cikin dakin zuciyarta sai faman sheka dariya take yi son ranta. Shikuwa Bello tunda ta saka kai ta fice daga cikin dakin duk yaji komai ya jagule masa shiru yayi yama nazarin maganarta tun yana tsaye har ya koma zaune ya zabga uban tagumi komai yake ji ya kwance masa tufkar da yake yi sai faman warwarewa take yi komai ya kwance masa lokaci-lokaci yake ajje numfashi idanuwanta na kan Habeeba wacce ke takure waje guda ya rasa a ina zai ajje wannan lamarin nata ya rasa me ke damunta likita yace masa lafiya ta haihu amma ya za ayi ace kuma magana ta gagareta yi a karan kanta me haka ke nufi ya kamata ace anyi duba a wannan lamarin sake ajje numfashi yayi ya shi tambayar kan sa abubuwa wanda ko wuka a makoshi zai gani ba shi da amsoshin su sun jima cikin wannan yanayi har dare ya fara shigowa ka fara kiraye kiranyen Sallaha hakan ne ya fargar dasu daga duniyar tunanin da suka lulaƙa da sauei Bello ya mike yana mai duban Habeeba wanda idon ta yake ƙyar sama ko ƙiftawa ba tayi hakan ya dan fadar masa da gaba da sauri ya isa gareta ya dafata gami sa girgizawa sai yaga ta saki ajiya zuciya gami da lumshe idanuwanta wasu hawaye ne suka surnano mata a kunci hakan yay matukar sanya gabansa faduwa da sauri ya zauna kusa da ita yana kokarin tallabo ta. "Sannu Habeeba me ke samun ki, fada mani don Allah". yana magana bakin sa na rawa amma ita ba alamun za ta yi masa wata magana illa kafeshi da ido da tayi. "kiyi magana mana sanar dani abin da ke damun ki". numfashi idanuwa tayi lokaci guda jikinta yayi wani irin fizga shi kansa Bello sai da jikinsa yayi rawa da sauri ya zabura yana mai faman jinjigata yana ambaton sunanta amma ba ta yi magana kuma ba ta buɗe idanunwata illa kirjinta dake bugawa kadan-kadan da sauri ya duba in da Mariya ke zaune amma bai ganta ba sam bai lura da ita kusa dashi tsaye ba idanuwanta na faman zubar hawaye "sai da nace a mai data Asibiti amma a kace ai magana ta akwai yarinta a cikinta wanda ni A KARAN KAINA na san maganata tana sahun da za ajerata a maganganun da za ayi amfani da su domin ceto Ummata". Sosai yake dubanta yana kallon yarda hawaye ke safah da marwah akan fuskarta tausayinta yaji yana tsargar masa ko ina na jikinta yana ganin rashin dacewa da kuma kin yarda da yayi da maganar 'yarsa wacce ta cancani ace an dubata kuma an daurata a mizanin hankali amma bai yi haka ba har sai da ta budi maki ta nuna alamun kin yarda da kayi da ita. "Mariya ban ki ta taki ba amma ai abin lura nan shine kina jin abinda Goggo Marka ta fadi kan wannan lamarin kin ga ai bai dace ace anyi gangawar mai da ita Asibiti ba domin tun acan ya kamata ace sun sanar damu abinda ke faruwa amma suka ce damu ba komai". tun da ya fara magana take dubansa cikin wani irin yanayi da yarda furucin nasa ke sauka wanda ta tabbata ba a son ran sa yake yin sa ba kawai FIN KARFI ake nuna masa wanda haka sam ba zai haifar musu da ɗa mai idanu ba. nisawa tayi hawaye na kara samun mazauni a fuskar ta. "ceton rai daban yake a wajan dangin rai ko wani hali kake ciki in har kana da damar ceton wami rai ko ba makusancin ka ba zaka iya don Allah baba na rokeka mu mai da Umma Asibiti". "kiyi hakuri sa kukan haka nan za a mai da ita". Girgiza kai kawai take yi domin ba ta ga alamun Eh da gaske za ayi hakan ba kawai magana ce akayi ta wacce sam ba alamun za ayi ta a aikace jinjina kai ta shiga yi tana faman sauke numfashi a hankali cikin jan jiki ta fice daga cikin dakin domin ta tabbata in har ta cigaba da tsayuwa cikin dakin komai zai iya faruwa da ita ba za ta iya cigaba da ganin mahaifiyarta cikin wannan hali ba. Tana fita waje ta hango Goggo Marka zaune kofar dakinta sao faman kai lomar abincin takeyi bakinta wanda ta tabbata daga gidansu Hafsatu aka kawo mata shi ko kuma taje da kanta ta amso da sauri ta kau da kanta domin bata ga amfanin kallon nata ba illa ya kara mata wani takaicin a zucci. "wai har yanzun Habeeba ba tayi maganar ba?". Kamar daga sama ta tsinkayo muryar Goggo Marka tana tambayarta wani haushi ne ya zo mata wuya domin ita dai ba ta ga amfanin wannan tambayar ba ya za ayi kana cikin gida tare da mutum amma kuma kake tambayar ya yake kai da ya kamata ace sai sai wani ya tambayeka gyada kai tayi kamar ba zata tanka ba amma sai kuma ta fara kokarin motsa baki domin amsa mata 'ta ce mi' ta ji wani bangare na zuciyarta tace da ita haka sai tayi gum da bakinta tashiga tsayuwa a kofar dakin domin ita dai ba ta san abin yi ba akan wannan lamarin da ta rasa dame zata fassara shi cikin duniyar rayuwarta "ai wuya makarantar kare ce duk wanda ya ki ji ba ya ki gani ba nidai iyakata ido kuma fadan da yafi karfin ka dadin kallo gareshi". Goggo Marka ta sake fadi tana mai kai loman abinci bakinta takaici ya kume Mariya ji take kamar ta daura hannu aka ta kurma ihu da wannan jirwayen gami da shaguɓe da ake antayo mata duban Goggo Marka tayi tana mai faman kada kai ba shiri ta juya ta koma cikin daki abu dai gashi nan ya zame mata goma da ashirin ta rasa ma ina zata dosa da wannan lamarin. Haka suka rayu cikin wannan dare tsayin lokaci ko wanne zuciyarsa sam ba kayan jin dadi cikinta komai yayi musu kunci abubuwa maras dadi sai faman wuntsulowa suke yi cikin rayuwarsu cikin lokaci kankani ƙaddara ta juya akalar rayuwarsu zuwa wani fikire wanda ba su taba tsammani ba za su kai gareshi. A daran Mariya tayi kuma matsananci domin kuwa yanayin da ta ga mahaifiyarta a ciki gabadaya susuta ta, ta rasa mai ke yi mata dadi cikin rayuwa bala'in take gani ya na tunkaro mata wanda take tsammani komai na rayuwarta zai iya raguzama mata shi duk wani kudiri da buri da ta daukar wa kanta cikin duniyar rayuwarta ta fara hango rashin tabbatuwarsa tana hango wata bahaguwar ƙaddara na kokarin tafiya da komai nata na jindadi tana kallon yarda ƙaddara ke kokarin sauya mata akalar yarintar ta wanda ta rasa hanyar da za tabi domin dawo da komai a cikin wannan dare. Nishi take yi kamar mai kokarin haifo ɗa ta direshi a duniyar nan wani abu ne taji yana tokare mata kirji duk sa'ilin da ta ji Ummanta na fizga kamar wacce aka jonawa wuyar wuta take fizgarta. "Baba kun ki kamar uzuri ne wallahi uzuri na yana da matukar amfani lokaci tafiya yake yi kuma ba waiwayo mu zai yi ba na rokeka da mu nemi abin yi". Magana take yi muryarta na kokarin bayyanar da kukan da take boyewa a zucci laɓɓanta sai faman rawa sukeyi ba ta jin tausayin kanta kamar yarda take tausayin dangin rai din nan gudawa biyo domin yalwar kwanciyar hankalinsu shi ne nata. "Mariya nayi kuskure da na sani tun waccan lokaci na dauki maganarki...". Da sauri ta mike jikinta na rawa sosai ta isa gareshi. "wallahi yanzun ma lokaci bai kure ba na rantse maka da Allah Baba ka taimaka ka tashi mu tafi mu ceton ran da yake da abubuwan taimakawa sosai a rayuwarmu". Ido sosai ya zuba mata yarda yake ganin tausayi da jin kai cikin idanuwan Mariya hakan ya kara narkar masa da zuciya cikin tausayinta yana kallon rashin hayyaci yarda yake da wainiya da ita amma karfin zuciya kawai da ikon Allah ke bata kwarin aiwatar da komai in ba don haka ba komai zai iya faruwa da ita. "mu bari gari ya waye Mariya dare yayi sosai". Sosai Mariya ta kureshi da idanuwanta jikinta lokaci guda ya saki ta zube a kasa kamar wani kayan wanki da aka yasar hannu biyu duk ta daura bisa kanta kamar mai shirin kurma ihu amma hakan ya gagara safiyar da taji ya ambata yafi komai kawo mata tashin hankali cikin rayuwarta a wannan Daren ga take yi kamar KAFIN SAFIYA komai zai iya faruwa kundin ƙaddararta zai iya buɗe mata wani shafin wanda bata tsammani zata iya karance shi balle kuma ace hadda za tayi duban su ta shiga yi duk su biyun idanuwanta na faman hargitsewa kamar wacce ya tuntuli barasa ta kai ma karo hannu ta sauke daga saman kanta ganin ihun yaki zuwa ta kurma shi ta gumi ta zuba hannu bibbiyu sai walanniya take yi da idanuwanta. [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA. *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA BAKWAI. Misalin karfe shidda da rabi suka isa cikin Asibiti bayan sun kwashi dirama ta kin karawa da Goggo Marka inda ta hau ta dire tace ba ta san zancen ba ba wanda ya isa ya koma da Habeeba Asibiti a karasa kashe ta mutane da yawa suka taru yarda kasan an kamo gobara ce ta kama gidan ba ka jin muryar kowa sai ta ta. "kasan Allah ba za a je da ita Asibitin nan ba ka na kallon yarda kuka je da ita lafiya kalau amma daga dawowarku ko magana ba ta iyayi balle aji abin dake dawainiya da ita ka ga hakan na nuni da zuwa Asibiti ba shi da amfaninin komai illa a kai mace a kashe ta tun lokacin ta bai yi ba". Tun da gari ya waye Mariya ke rusar kuka kamar ranta zai fice daga jikinta komai ya kwance mata musamman yarda ta ga Goggo Marka na nunawa a gareta da uwarta na halin-ko-in-kula sosai take jin bacin rai da takaici sosai taken jin komai na kwance mata na duniyarta rarrashi da ban baki ba wanda ba yi tsakanin Babanta da Goggo Marka ba amma saboda kin jini da rashin son gaskiya haka ta tunkuɗeta daga jikin ta ta na faman zazzaga ruwan BALA'I. "ke dalla janye daga jiki ko na buge ki 'ya sai shegen makirci da munafurci duk kece ummul-aba'isin faruwar komai kuma wallahi zan ga yarda za a fidda Habeeba da ga gidan nan a mai da ita wajan wanda za suk kashe ta a banza a wofi". A fusace Bello ya shiga dakin Goggo Marka in da ta janye Habeeba tun da safiya ta waye taji suna shirin mai da ita Asibiti zaune ya tadda ta jikinta sai faman mazariya yake idanuwanta na faman zubda hawaye fuskarta ta duk ta kumbure da sauri ya isa gareta jikin sa na rawa ya dago gabadaya kamar wata 'yar tsana ya yo waje da ita nan mutane suka rufa masa baya lura da sukayi Goggo Marka na kokarin hanawa daƙyar da soɗin goshi a ka fidda ita aka saka a Napep Mariya da Bello suka shiga mai Napep din ya ja aka bar Goggo Marka a nan tana ta faman zazzagawa ruwan bala'i ita ala'dole son Habeeba take yi ba ta so a kai ta inda za a kashe ta ba ta duk mutane kallon ta suke ba sun mai da ita wata mahaukaciya. Lokacin da suka isa Asibitin ba su tadda likita ba don a ranar bai zo aiki asibitin ba ya tafi can cikin garin Minna (General hospital) domin gudanar da wani aiyuka Nurses kawai suka samu kafin su amshe sai da suka gama yi musu tambayoyin ya akayi suka zo duniya sunyi matukar kuluwa musamman Mariya don ji take kamar ta shake wata figaggiyar Nurses mai zubin mociya ita ce kan gaba wajan jera musu tambayoyi sai da Bello ya shiga hada su da Allah da Annabi sannan suka amsi Habeeba cikin matsanancin halin da take ciki sun ba su gado sai da kuma abin da za ayi mata ne ya gagra domin tunda Nurses suka ba su gado suka je suyi zaman jiran likita har ya dawo sannan ya dubata su kam ba su san abin da za a suyi mata ba. Mariya ce ta dubi mahaifinta bayan sun shafe sama da minti talatin ba wani canji tunda suka zo ko ta kan su ba a sake bi ba hakan ya kara shigan da su halin kaka ni kayi domin dai ga Habeeba nan akwance yarda take hakan take illa lokaci-lokaci tana figza. "Baba nikam mai zai hana mu kaita wani asibitin tun da nan din likitan bayanan?". ta fadi tana mai goge idaniwanta da suka gaji da zubar hawaye. Zabura yayi jin abinda tace domin tun dazu tunanin da yake tai kenan amma saboda rashin madafa shiyasa ba nemi hakan ba domin ko yace zai dauke zuwa wani asibitin ya san dole a bukaci kudi wanda shi ya tabbata ko wuka za a saka masa a makoshi bai maganin ko taro domin ko Napep din da suka hau bashi ya biya ba bai san ma wa ya ba mai Napep din kudinsa ba shi ya ga ya na sauke su ya ja abinsa yayi gaba zuwan su asibiti yayi ne kawai saboda rashin abin yi bai san yarda za su kasance ba in likita ya zo bai san me zai ce dashi ba. "Don Allah Baba". ta sake fadi ganin da tayi kamar bai yi amanna da maganar ta ta ba. Gyada kai yayi yana mai sauke ganinsa ga Habeeba sannam ya juyo ya kalle ta. "naji ki Mariya amma kuma...". Sai yayi shiru yana kureta da idanunsa sa kafin ya sauke wami gumi da yaji ya keto masa lokaci guda. Ita ma kallonsa take yi sosai da sosai cikin rashin fahimtar in da maganarsa ta dosa sai ta shiga gyaɗa kai. "Mariya ba ni da hali, babu komai a gareni, komai ya kare". Sosai take kallon yarda yarda yake maganar kamar mai son fashewa da kuka maganar yake saki kamar ana rike masa kuzarin harsheksa komai da yake fadi kawai fadi yakeyi cikin rashin abin yi zuciyarsa da ruhinsa a hargitse suke dalilin rashin in da zai sa gaba baya so ace ya nuna rashin jarumta a wannan lamarin ba ya so a ga gazawar so ya ya ne amma ba yarda zai yi sosai yake jin kunar zuciya da yarda yake jin wani makakin takaici da bakin ciki da suke tsarkewa waje guda cikin duniyar rayuwarsa cikin kankamin lokaci yana kallo yarda ƙaddara take kokarin buɗe masa sabon shafi na rashin dadi nisawa ya sake yi akaro na ba a dadi har izuwa lokacin. idanuwan Mariya na kansa tana kallon yarda komai ke sauya ga mahaifinta tana kallon yarda komai ke canza salo cikin rayuwarsa cikin kankanin lokaci ina ma ace tana da wata dama wacce zata yi amfani da ita domin taimakon rayuwarsu ina ma ina ma. Haka tai ta saƙar zuci abubuwa da yawa take kudiri da buri cikin duniyar rayuwarta wadanda tayi kasafinsu cikin kankanin lokaci. "na sani Baba amma rashin babu ba zai hana ku ki kai ta wajan da za a bata kulawa ba, kawai mu dauke mu kai ta wani asibitin duƙ da dai ba mu san yarda zata kasance ba, zaman namu hakan ba komai zai kara mana ba illa shiga wani ruɗanin". Gyaɗa kai yayi ba tare da ya tanka ba domin ya rasa me ma zai ce sun jima cikin halin shiru kafin ya kokarta motsa laɓɓansa. "mu kara hakuri, bari naje naji ko ya kusan isowa". ya fadi yana mai kokarin mikewa cikin sanyin jiki ya fice daga cikin dakin. Mariya ta bishi da kallo kallon tausayin su baki daya tana kallon yarda lokaci guda komai yake kokarin kara riccaɓe musu a duniyarsu tana kallon yarda rashin babu yake kokarin hana komai ya tafi yarda ya kamata a cikin duniyar su ta sani ba su dashi kuma ba in da za su je su samu ba su da wata kadara ta a zo a gani da za su saida tayi musu maganin abin da ke damun su sosai take jin tausayin kan su tana tuno irin rayuwar da suke ciki tun kafin wannan ƙaddara ta fara kokarin ruguzu musu cikin rayuwa ta sani babu tayi matukar taka rawa wajan wanzar da komai a duniyar rayuwarsu ta sani ba su dashi komai ma babu su dashi duk da hakan suna godewa Allah da ya ara musu numfashi cikin duniyar nan har suke rayuwa kala daban-daban. Hannu ta sanya ta dauke hawayem da suke ta faman zubo mata ba tare da ta hannusu ba ta sani lokacin su ne yayi suna da damar zuba yarda suke so duk da dai ta san zubar na su ba wani abu ne da zai taimaka wajan hana wanzuwar komai ba. duban Ummanta take yi tana faman gyada kai tana kallon yarda Ummanta ta sauya lokaci guda tana kallon yarda Ummanta komai na ta ya sauya wanda za ta iya cewa ba ta da bambanci da GAWA DA RAI eh mana gawa da rai duk mutumin da zai rasa bakin magana ko wani abin yi yana zaune waje guda shi kansa bai san waye shi ba bai san me ke damun sa ba zai iya fadar matsalar sa ba ai ko za a iya kiransa da haka din. "nima za ki iya buɗe baki Umma ki fadi abin da ke damun ki, ina ma ace zaki iya kwatanta mani abin da ki ke ji a jikin ki da kuma abin da ya assasa rashin maganarki". Sosai taji kuka na taho mata hakan ya sanyata saurin yin shiru gami da rufe bakinta da tafukan hannayenta sai faman girgiza kai take yi kukan na kara kokarin sautin bayyana mikewa tayi ta isa gareta cikin hanzari ta kankameta sosai kamar zata koma ciki kuka take yi sosai mai cike da rauni da karayar zucci kuka take yi mai matukar bai wa mai sauraro tausayi da jin kai kuka ne take yi kamar ranta zai fita. "Umma bana so haka ta kasance a gareki bana so ki kasance cikin rayuwa a haka bana so na ganki a haka har iyakar numfashi a duniyar nan. Ina son ganin ki kamar yarda kike a da koma fiye da haka don Allah Umma don Allah na rokeki". Tun da ya tun karo dakin yake jin sautin kukanta kukan da ya sanyi jikinsa sanyi ya samya zuciyarsa cikin wani irin yanayi lokaci guda tausayi gami da jikan 'ƴar da matarsa gabadaya sun gama galabaitar dashi lokaci guda a duniyar rayuwarsa sosai yake jin zuciyarsa na kuna sosai yake jin kirjin sa na bugawa a dukkan wani karan sautin kukan Mariya in yaji. Wai shin ya zai yi ne, me ya kamata yayi ne?. Tsayin dakiku ya shafe a wajan kafin ya fara jan jiki domin isa cikin dakin sosai yake jin faduwar gabansa na daduwa sosai yake jin ko ina na jikinsa na canza sautin rayuwa sosai da sosai yake jn wani yanayi na rashin dadi na ywo da shi a sama a gajiye ya isa cikin dakin yanayin da yaga Mariya rungume da Ummanta yanayin da yake kallon kwayar idonta ta canza gabadaya izuwa ja fuskarta ta fara canzawa ita kanta da sauri ya isa gareta cikin tashin hankali a idanuwansa. "Mariya!". ya ambataci sunan cikin wani irin sauti mai dauke da rauni da amon sauti. "don Allah Baba don Allah na rokeka". abin da ta ke fadi kenan cikin sautin kuka ta yo kasa gabadaya ta dafa kafafuwansa sosai yake jin zafin hawayenta dake zuba akan fatar kafarsa sosai yake jin tausayinta. "na rokeka ka taimaka...". "Mariyaaa". ya sake fadi cikin sauti sosai. Hannu ya saka ya dagota gbadayanta ya hadata da jikinta ya shiga bubbugawa a hankali cikin sigar rarrashi. "Shiru Mariya kiyi shiru, komai zai zo karshe, likitan ya dawo yanzu...yanzu haka yace zai zo kiyi shiru". kawai magana yake yi cikin yanayi na karfin zuciya da ya ruhi sosai yake ajje numfashi ga duk wata kalma in ya furta ta. A hankali ta dago manyan idanuwanta wanda suka canza kala tana mai kallon sa sosai tana son gasgata abin da take ji yana amsa amo a kunnuwanta da kwakwalwarta sosai take jin saukar kowa kalma da yake furtawa ba tare da tace komai ba ta zare jikinta daga nasa tana ja da baya a hankali sosai tayi nisa dashi har ta kai bakin kofar ta kwasa da gudu tayi waje. kallo kofar da ta fita yake yi zuciyar cike da fargbar in da ta dosa da sauri ya fara kokarin barin dakin amma sai ya tsaya cak! Motsin da yaji da sauri ya juya Habeeba ce ke kara takure kanta waje daya sosai yake kallon yanayin da ya ga tana yiwa jikinta kamar wacce ake kokarin zarewa wani abu dunkulewa take yi waje guda har sai da ta jingina da bangon dake kusa da gadon da take gyada kai yake yi ya rasa dalili ya rasa me hakan ke nufi ya rasa in da zai saka lamarin ya gano ME KE FARUWA? sosai ya rasa komai na tunanin sa lokaci guda sosai yake jin tausayinta na kara samun gurbi a zuciyarsa kau da kai yayi saboda in har ya cigaba da kallon ta hawayensa za su iya zuba bayan HAWAYEN ZUCIYA da yake ta faman dambe da su amma sun ki tsaya. da hanzari ya doshi kofar ficewa daga cikin dakin tafiya yake yi cikin ikon Rabbi! sosai yake jin komai na canza ji yake yi ina komai zai fice daga jikin Habeeba ya dawo masa ina ma inama. da wannan zancen zucci ya isa harabar asibitin ya shiga rarraba idanu domin hango Mariya amma ba alamun ko da mai kama da ita ne bai hanga ba da sauri ya fara nufar kofar Get din domin fita waje cak! ya tsaya muryarta da ta keto cikin iska ta kawo wa kunnuwansa duka nan ya shiga waige waige domin canko inda ya ji sautin muryarta ta mai dauke tausayi sosai har ma da kuka a cikinta. Idanuwansa ne sukayo waje gabadaya gaban sa yayi wani irin bugu sosai har sai da ya kai hannunsa saitin kirjinsa Mariya ya hango ta na biye da likita kamar wacce za ta kifa domin roko da take yi da hannayenta duk biyu idanuwanta na fidda hawaye sosai shi kuwa likitan sai faman tafiya yakeyi kamar bai wata halitta mai daraja na biye dashi ba sosai yayi kunnan uwar shegu da ita rintse idanuwansa yayi ji yake yi wannan lamari kamar ba gaske ba jin komai yake yi kamar a mafarki. "Yaa Rabbi!!". ya furta yana mai dafe kansa sosai ji yake yi yana juya masa 'yar sa ta cikinsa take bin wani yana yarfata yana wulakantawa 'yarsa gudan jininsa kaico ba ya fata hakan ya tabbata ba ya kaunar haka ko a mafarki a halinsa su kasance a haka baya fatan rashin babunsa ya sanya ahalinsa cikin wannan irin hali na kaskaci da wulakantawa a hankali yake kokarin bude idanuwansa yana rokon Allah kar ya sake ganin wannan kaskancin. Girgiza kai ya shiga yi lokacin da ya buɗe idanuwansa ba tare da yayi arba da mugun ganin da yayi dazu ba da sauri jikinsa na ɓari ya koma cikin asibitin dakin da Habeeba take ya dosa yana jin kunar rai sosai bakin ciki takaici duk sun samu mazauni cikin ransa. Cikin wannan yanayi ya isa dakin tun a bakin kofa ya ja birki yayi turus! idanuwansa sosai sukayo waje likita yake gani da Mariya tsaye kan Habeeba jikin Mariya sai rawa yake yi sosai da sosai takaicin sa ya kara daduwa lokacin da ya lura da irin kallon da likitan ke wa Habeeba hannunsa a harɗe. *"eclampsia".* Abin ya likitan ya fadi kenan ya na faman gyada kai yana kyaɓe fuska kamar wanda ya ga wani abun ki. Mariya da sauri ta dubeshi lokacin da taji yayi magana sosai take kallonsa kamar mai son karin bayani bata fuskanci abin da yace ba bata gane me yake nufi da kalmar da ya furta. Nisawa tayi tana kara kureshi da ido shi kuwa sai faman jinjiga kai yake yi har zuwa wannan lokacin hannunsa na harɗe a kirjin sa. laɓɓanta ta motsa alamun son yin magana. "Uhmm...". Sai kuma tayi shiru ganin irin kallon da ya cilla mata. "ai kin ji abin da na ce ko?". ya fadi gami da daga mata girarsa. Da sauri ta shiga gyada kai alamun a,a ba ta fahimci mai yace ba amma sai ya nuna ko a jikinsa domin shi ana nashi bahagon tunanin nuni tayi masa ta fahimta daga kafada yayi gami da juyawa domin ficewa daga cikin dakin. "Likita!". Mariya ta fadi cikin sauti mai dauke da rauni sosai kafin ta dora da cewa. "Taimako don Allah na rokeka". ta karashe tana mai hada hannayenta waje guda alamun roko idanuwanta cike da kwalla. Sosai yake kallonta bayan ya tsaya jin ta kirasa idanuwansa manya jajaye ya sauke akanta yana faman gyada kai kafin ya saki nishi kofofin hancin sa duk suka buɗe gabadaya kamar wanda ya gaji da gudu fuskar nan tasa bakinkirin sai faman yatsine ta yake yi gami da tabe bakinsa mai kama da jikankiyar ganda. "Me ki ke so nayi miki yanzu?". ya fadi ya na shafar runbuɗeɗan cikinsa mai kama da cikin yan tagwaye wata tara. Rausayar da kai tayi kwallar da take makalewa suka zobo a kuncinta. "Taimako don Allah...". "Taimako fa kika ce, nikam wani irin taimako zan yi miki a yanzu?". Sosai taji gabanta ya buga jin irin kalamansa da kuma nuna halin-ko-in-kula da ya nuna akan ta da kuma maganarta hawaye taji sun sake balle mata ta rasa mai kuma ya dace tayi lallami da ban bakin ta duk sun kare iyakar roko dai ta nema a wajan sa amma duk hakan bai saka ya jikanta ba ko ya ya ne sai kace mara imani da tausai a ran sa gyada kai ta sake yi tana dubanda har da wani murmushi ta saki wanda ita kanta ba ta san daga ina ya fito ba bata san amfanin yin sa ba illa wani kullin abu da taji ya tokare mata zuciya da ruhi. "Uhmma ban san mai zan ce da kai ba kuma amma... Uhmma taimako dai nake nema". ta karasa tana mai sake kai hannu bakinta domin wani irin kuka ne taji yana tasowa tun daga ruhi da zuciyarta yana kokarin samun masaukin a laɓɓanta da sauri ta kallo da kai daga kallonsa sosai take jin haushi a zuciyarta haushi akan likitan da bashi da tausai ko ya ya ne a zuciyarsa ba imani. Kallon ta yake yi da irin halin da take ciki sosai yake jin wani abu a ransa amma sai ya kau dashi da sauri gami da jan tsaki ya juya cikin sassarfa yana kokarin barin cikin dakin. A bakin kofa ya ci karo dashi tsaye fuskarsa a tamke kamar bai taba wani abu wai shi murmushi ba sosai yake kallon likatan ciin yanayi haushi da takaicin abin da yayi wa 'yarsa sosai yake ji kamar ya shako wuyarsa ya hada da bango domin ban ga amfanin sa ba, ba irin wadannan mutanen ake so cikin aikin likitanci ba, ba irin wadannan mutanan ake so a wajan taimako da jin kai gami da tausai ba. Haka ya cigaba da kallonda har ya rabashi ya wuce ba tare da ya tanka masa ba illa wani irin mugun kallon tsana da yake bin sa dashi ransa a matukar bace ya juyo yana duban Mariya wacce take tsaye waje daya kamar wacce aka dasa sai faman sharar kwalla take yi. "Me ki kayi kenan Mariya, ina amfanin haka wa yace miki irin wadannan mutanan ake neman taimako wa wajansu?". rintse idanu tayi wani ɗaci take ji tun daga kasar ruhinta har zuwa zuciyar. "na rasa ya za nayi ne, komai ya kwance mani na dauƙa duk mutane iri daya ne a duniyarnan in kaje neman taimako za suyi maka". ta karashe tana mai tura laɓɓanta cikin baki gabadaya tana cizawa sosai take jin haushin kanta duk da karancin shekarun ta amma hakan bai hanata jin daci a ranta ba akan abin da bakin mutumin nan mai kama da gwanki ya yi mata ta tsane shi tsana mai tsana ni a rayuwarta ko fuskarsa bata muradin sake gani. "in jiwa ya fada miki mutane iri daya ne? A halinta ne suke iri daya amma a DABI'A da hali suna da bambanci sosai da sosai". Sosai take jin kalaman mahaifinta na shiga cikin kunnuwanta tana fahimtarsu daya bayan daya tana gasgatawa. 'na tsane shi bana son sake ganin sa, ko A MAFARKINA' abin da ta ambata kenan cikin kunar rai a zuciyarta tana mai faman dauke hawayen fuskarta "ina kika ganshi har kike kokarin shiga wani yanayi na rashin jindadi rai". gyada kai tayi kamar ba zata amsa masa ba can kuma ta nisa. "na dauka shine likitan da ake jira shiyasa naje na sameshi da kaina domin ganin da nayi lokaci tafiya yake yi". ta karashe tana mai yamutse fuska gami da yarfar da hannu. Sosai ya fuskanci in da ta dosa tunaninta shine likitan da aka ce zai zo ya duba Ummanta. "ni ban ma san shi ba ko da na kawo Ummanki ba shi bane ya dubata wani daban ne...". Sallamar Dr.Aqeel ne ya sanyashi saurin jinkirta zancen sa ya mai da idanuwansa gareshi ita ma Mariya duban mutumin da yashigo takeyi wanda lokaci guda tayi amanna shine likitan da Babanta ke magana. "Sannunku ko, ya mai jikin?". abin da Dr.Aqeel kenan yake fada fuskarsa na bayyanar da yanayin jimami da sauri ya isa ga Habeeba sosai da sosai yake dubata tsayin wani lokaci kafin ya saki ajiyar zuciya ya dubi Bello da Mariya cikin fuskar tausai "Uhmm...". Abin da yayi kenan cikin cizon laɓɓa yana mai sake duban su. da sauri Mariya ta isa gareshi. "Uhmm Likita don Allah...". "karki damu na san halin da kuke ciki dukkan ku kuyi hakuri dole ku shiga damuwa da tashin hankali musamman lamari irin wannan wanda ba ku san ina ya dosa ba eclampsia take fama dashi". Sosai kalmar da ya furta tashiga yi musu yawo akai cikin rashin fahimtar kalmar wacce lokaci guda Mariya ta gano irin wanda waccan bakin mugun ne ya fadi dazu amma kuma ba ta san me nene ba bata san mai kalmar ke nufi ba?. [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA. *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA TAKWAS. Sun jima cikin shiru aka rasa mai tankawa a cikinsu, domin sun saki baki ne suna jiran cewar Likita. kamar yarda shima yayi shiru, yana nazarin ta inda zai fara yi musu bayanin lamarin. Ihun da ya karaɗe dakin ne ya dawo da su daga duniyar shiru da na tunanunnuka da suka faɗa a firgice duk sukayi kanta cikin matsanancin tashin hankali sosai take ihu gami da fizge fizge tana hada kanta da karfen gadon da take hannayenta duk biyu ta rufe kunnuwanta da su da sauri Mariya ta isa gareta tana kokarin rike amma wani wawan fizga da tai gabadaya Mariya tayi kasa ta zube hakan da Bello ya gani da sauri ya isa gareta da taimakon likita shiga kokarin riketa amma ina! wani karfi ne ya ke zuwa mata lokaci guda sosai take fizge fizge su kan su sun rasa yarda za suyi su riketa sai da sukayi da gaske sannan Bello ya samu da kyar ya rike hannayenta ya hadata da jiminsa ta kankame amma gabadayam su sai jikinsu ya kara shiga wani irin shock kamar an jona su da wayar wutar nepa sai mazari jikinsu ke yi. Da ƙyar da soɗin goshi suka samu fizge fizgen nata ya ragu dalilin irin rikon da Bello yayi mata ba na wasa bane. Kuka ne ya sake karaɗe dakin amma wannan karo kukan yao ne dake cam yashe wanda sam suka manta da lamarin sa tun da suka shigo Asibitin. Gabadaya sun manta dashi, sun manta sun zo da wani dangin rai bayan su gabadaya suka juya suna kallon daga in da kukan yake tasowa suka shiga kallon-kallo a tsakaninsu. Mariya ce ta mike da gudu cikin tsananin faduwar gaba ta isa gareshi ta sungomo shi gami da haɗeshi da jikinta wani irin tausayin sa da kauna taji yana kara wanzuwa cikin jikinta sosai take jin tausayin sa hawaye sai zuba suke saman fuskarta suka gangarowa bayansa gyaɗa kai kawai take yi komai gani take yi yana faruwa kawai amma ta rasa komai na hayyacinta komai kara rikice mata yake yi. "Yaa Rabbi!". ta fadi cikin tashin hankali kafin ta fara tafiya cikin ɓarin jiki ta isa ga Doctor dake ta faman kokarin ganin Habeeba ta daina fizge-fizgen da take yi. "Likita Taimako don Allah kar bugun yayi yawa na tabbata in dukan yayi yawa komai zai kara jagulewa kanina don Allah ina bukatar rayuwarsa shima shi kadaine dan'uwa na a duniyar nan uwa daya uba daya...". ta tsahirta da maganar da take yi kirjinta taji yayi mata nauyi sosai da sosai kafin ta sake kokarta daga laɓɓanta. "Tun da ya zo duniyar nan..ya fara cikin karo da komai da komai na rashin jin dadi ko..ko abinci bai iya samun ci ba a duniyar nan". yanayin sautin da ta ajje furucinta dauke da kuka yayi matukar shigar da likita cikin wani irin yanayi da sauri Dr, Aqeel ya dago kan sa dake wajan Habeeba wacce izuwa wannan lokacin fizgar da take yi ya lafa illa numfashi mai karfi da take ta faman ajjewa. Sosai yake kallon Mariya yana jin tausayinta na shiga ko wani lungu da saƙo na jinka sa numfashi ya ajje ya na duban Bello a hankali ya furta. "Gaskiya ne wai haka ba ku ba shi komai ba?". Gyada kai ya shiga yi domin bai san abin da zai ce da Dr.Aqeel ba. bashi da abin cewa komai ya sauya masa tunani hankalinsa na kan Habeeba ya sani yana son ɗansa amma kuma ita rayuwarta ya fi so sosai da sosai. "Uhmm amma likita...". Ido ya zaro waje sosai yana duban Bello cike da fargabar abin da yake sanar dashi wanda lokaci guda ya gasgata maganar Mariya. "Eh haka ne kenan?". Dr.Aqeel ya tambaya idanuwansa kafe akan Bello. kai ya shiga gyaɗa masa alamar haka sosai da sosai Dr.Aqeel abin ya taba masa zuciya tausayin jaririn yana ɗalsar masa a rai da ko ina na jikinsa da sauri ya waiga ya kalle shi hannun Mariya yanayin yarda yaga yasaka hannayensa a baki ya tabbatar masa da haka din. Da hanzari ya fice daga dakin ransa a bace cikin yanayin ganin rashin kulawarsu da nuna adalci ga ɗansu da suka haifa bai kamata ace ɗa jariri dan kwana daya ba ya fado duniya ya ci karo da horan yinwa ina wannan ba adalci ba ne sam!. "likita ana bashi ruwa fa". Bello ya fadi cikin ɗarɗar ganin yanayin da Dr.Aqeel ya nuna a fuskarsa hakan ya tabbatar masa ba su kyauta ba sam!. sarai! Dr.Aqeel ya ji abin da Bello ya fadi amma hakan bai rage masa jin haushin da yake yi akansa ba. Mintina goma ya shafe sannan ya koma cikin dakin hannunsa dauke da flas na jariri wacce take dauke da tatacciyar madara wacce ta samu hadi sosai sai gorar ruwa kuma shima dai da ka gani za ka gane na bukata jariri rai ne shigowarsa ya sanya Bello saurim miƙewa daga zaune da yake ya zabga tagumi hannu bibbiyu ita kuwa Mariya har wannan lokacin tana tsaye rungume da karirin. ko Kallon in da Bello yake bai yi ba ya doshi Mariya. "Zauna". ya fadi yana mai janyo mata kujera dake girke kusa da ita ba musu ta zauna idanuwanta akansa ganin yanayin da fuskarsa ta nuna na rashin wasa. Mika mata flas din yayi, ba musu ta sanya hannu ta amsa duk da dai ba ta san ya za tayi masa ba duk da dai ta fahimci abin da yake nufi da abin da ya bata sai dai ta ya ya za ta bude har tayi amfani dashi a dan tsora ce ta dube shi. "Uhmm ya zan yi?". bai tanka mata ba illa amsa da yayi ya buɗe mata gami da kaiwa bakin yaron sannan ya saki alamun ta riƙe da sauri ta rike ta sake gyara mata zama a bakin yaron kamar wanda yake ji a dora masa haba! ai sai ya shiga ja kamar zai tsinke bakin har wani sautin kara ke fita na tsotsa da yake yi dosai yake sha Mariya tana kafe da ido sai take jin tausayinsa ta na jin haushin rashin bashi abinci da ba su yi ba ta san laifin su ne a ciki sosai da sosai. Wata irin ajiyar zuciya ta saki mai karfi ta daga kanta ta dubi Dr. Aqeel da ya kure yaron da kallo yana jin tausayin sa sosai. "Godiya mai yawa likita". Dubanta yayi kafin ya dauke kansa ya fara taku daya bayan daya har ya isa ga Habeeba a daidai lokacin wata Nurse ta shigo hannunta dauke da wani farantin silba mai kyau sai dauƙar ido yake yi ta iso gaban Dr.Aqeel ta tsaya gami da rinsinawa alamun girmamawa. Hannu ya saka ya dauki abin gwaji da suke amfani dashi mai kama da iyafis sanyawa yayi a kunne sannan ya tunkari kirjin Habeeba da dayan bangaren abun a hannunsa ya dora sosai yayi shiru cikin natsuwa yana fahimta komai gami da gyada kai yana jujjuya idanuwansa tsayin wani lokaci kafin ya sauke ajiyar zuciya mai karfi ya zare abun idanuwansa akan Habeeba wacce itama idanuwanta a buɗe suke akansa a hankali ya dauko ledar ruwan (drap) dake kan faranti ya ratayeta akan dan dogon karfen dake girke a bakin gadon sannan ya dauko wata allura ya tsira cikin ruwan har guda biyu a hankali ya fara kokarin gyara mata hannu sosai yake kula da yanayinta bai som a samu wata mata yake yi a zuciyarsa a hankali ya tsira mata allura a jikin fatar hannunta yayi saitin komai yana kula da yanayin ruwan fara kokarin shiga jikinta sosai ya gyara mata komai kafin ya dube wanda ko gezau ba tayi ba da allurar ta shiga jikinta murmushi yayi wanda iyakarsa laɓɓan bakinsa. Bello da tun ɗazu yayi ka sake yana kallon sarautar Allah sai yanzu ya ajje numfashi har da 'yar guntuwar kwallarsa duban Dr.Aqeel yake sosai yake jin kaunar sa a ransa yana jin yarda jindadin abin da yayi masa yake ratsa masa zuciya bai san da wani baki zai masa godiya ba bai san da wani ido zai kalle shi yace dashi ya gode ba ya san duk wata godiya da zai masa tayi ƙanƙanta zai yo masa fatan alheri dafatan nasara cikin rayuwar duniya da lahira. shiru yayi sosai yana jin wani abu nayi masa yawo akai batun kudi dole ya nemo kudi domin yasan dole a bukaci kudi cikin lamarim nan gabansa ne ya yanke ya fadi lokaci guda ya shiga ambaton HASBULALLAHU WANI'IMAL WAKIL sosai yake jin tashin hankalin abin da zai faru nan gaba kadan me zai ce da wannan likitan mai mutunci da YAƘANA me zai ce dashi in ya dauko masa batun neman kudi. 'Yaa Rabbi!' ya ambata a zuciyarsa wani irin gumi ne yaji yana keto masa ta kowani kafar gashi dake jikinsa sosai yake jin gumin na gangara saman fatarsa sosai bugun zuciyarsa yake ji yana ɗaduwa "Raina ya baci matuka gaya akan abin da kuka aikata ga wannan rai da bai san komai ba a duniyar nan. Bai kamata ace daga fadowarsa ya fara gamu da BALA'I na horon yunwa bai ya kamata ace kun bashi kulawa a matsayinsa na wanda bai san kansa ba bai san wanene shi ba, bai san ya zai yi ya kula da kan sa ba, bai sam ya zai yi abu wani abu a rayuwarsa ba, sosai da sosai naji haushi". Ya karashe yana lanƙwasa yan yatsun hannunsa suna fidd sauti juya yayi ya dubi Mariya da ta kafe shi da idanu hannunta rike da flas din da alamun jaririn ya sha yayi nakas har yaji ba wani sauran gurbi da yayi saura a cikinsa da sauri ta sauke kai ganin yana kallonta. "me yasa kika daina bashi?". ya fadi yana mai da kallonsa ga yaron da yayi shiru yana lumshe ido kamar mai son bingirewa da bacci. Kanta akasa ta fara motsa laɓɓanta. "ya koshi ne na gani, ina sanya masa ya na turewa". Gyaɗa kai kawai yayi ya dubi Habeeba wacce a wannan lokaci bacci mai nauyi yayi gaba da ita. ajje numfashi yayi mai dan karfi. "wani hali muke ciki likita?". Bello ya kokarta fadi cikin rashin abin fadi, yanayin da yayi maganar gabansa na bugu kadan kadan domin bai san amsar da za a bashi ba. "sosai take cikin damuwa sosai rayuwarta ke cikin matsala sosai komai na rashin jindadi yake yawo a duniyar rayuwarta na san ka san haka". Dr.Aqeel ya fadi yana mai kafeshi da ido kallo ne yake yi masa na TUHUMA da son karin bayani da kuma son samun wasu abubuwa masu kama da satar amsa akan lamarin. Shiru yayi abubuwa da yawa suke dawo masa akai game da Habeeɓa da irin halin da yasan tana ciki na rashin jindadin rayuwa da damuwa kuma dake ci mata dunduniyar duniyarta gyada kai yayi gami da duban Habeeba sosai yake jin tausayin ta a ransa da ma jiki baki daya. "Haka ne". ya fadi cikin raunin Murya. "mai yasa haka, meye dalilin faruwar haka, kasan kuwa illar dake samu mace mai ciki in tana cikin damuwa kasan wahalar kuwa da take gamuwa da ita kasan irin kuncin rayuwar da take shi kuwa...". Ya tsahirta da zancen nasa ya na faman ajje numfashi. "ba kuyi mata adalci ba a rayuwa sam! ya kamata ace tana samun kulawa da kwanciyar hankali a gareku da kuke kusanci da ita sosai da sosai ba ma wannan ba yanzu kusan halin kuwa sa take ciki kusan abin da ke tafe da rayuwarta yanzu kuwa to a gaskiya komai zai iya faruwa da ita a kowani irin lokaci". "kamar ya?". Mariya ta furta ba tare da tashirya yin furucin ba zumbur ta mike tsaye idanuwa warwaje take duban Dr.Aqeel sosai take jin maganganunsa na saukar mata da tashin hankali mai matukar yawa zuciyarta ta shiga zarya kirjin ta na bugu sosai. "Don Allah...". "kiyi shiru tukunna". Dr.Aqeel ya tare ta daga maganar da ta dauko tun kafin ta dire. "ta gamu da cutar jinjiga wacce a turance ake kira da eclampsia a na samun tane dalilin yawan damuwa in har mai ciki tana da damuwa har tayi mata yawa ta kan haifar mata da cutar hawan jini daga wannan lokacin har zuwa lokacin da za ta haihu komai zai iya faruwa da ita har ya kasance bayan ta haihu ta gamu da cutar eclampsia wato ciwon jinjiga". ya tsahirta yana kallon su kamar yarda suma sukayi kasaƙe suna sauraron sa ya nisa gami da dorawa. "cutar ta kan kasance ga mai ita kamar ta hauka mutum mai cutar eclampsia ya kan kasance kamar mahaukaci komai yakan iya sauywa na rayuwarsa ya kan kasance mai fizge fizge ko kuma ya dinga zunduma ihu a ko wani lokaci a takaice dai duk macen da ta gamu da irin wannan cutar tan zama tamkar mahaukaciya". Sosai sautin kukan Mariya ke tashi cikin dakin kuka take yi wanda bai da sauti sosai amma hakan bai hana ya gauraye dakin ba sosai take jin tausayin Ummanta da ita kanta da Mahaifinta tun da Dr.Aqeel ya fara jawabin sa take jin komai na tashin hankali na wanzuwa gareta da sauri ta isa gareshi ta durkushe har tana kokarin sakin jaririn dake hannunta. "Don Allah karka ce Ummata ciwon hauka take yi don Allah likita na roke da ka taimaka kar Ummata da gamu da wannan BALA'In cikin duniyar rayuwarta komai zai iya faruwa da kta ba ita ka dai ba har da mu". Sosai kuka ya kwace mata tashiga yin sa kamar ranta zai fita. Ido kawai Dr.Aqeel ya zuba mata yana kallon halin da take ciki sosai da sosai yake jin tausayinta karamar yarinya kamar ta amma ta fara gamuwa da irin wannan laro tun kafin ta gama sanin ita wacece duban Bello yayi wanda shi gabadaya ya gama susucewa hannu bibbiyu ya sanya ya tallabe haɓarsa sosai yake jin komai na rashin dadi na wanzuwa a gareshi sosai yake jin HAWAYEN ZUCIYA na safa da marwa a gareshi domin duk jarumtakarsa na hana idaniyarsa ZUBAR HAWAYE bai hana zuciyarsa kokawa ba. A tausashe Dr.Aqeel ya sake dubansu cikin son kwantar musu da hankali. "Idan mace tana zuwa awon ciki akai akai likitoci kan yi saurin gano za ta iya kamuwa da eclampsia ta hauhawar jininta. Dan haka za su yi iya kokarinsu gurin ganin sun dakile aukuwar hakan, ta gurin ba ta shawarwari da kuma magunguna. Amma matan da basa zuwa awo sun fi kamuwa da cutar ta eclampsia mai kama da ciwon hauka. Duk da ce wa wasun ma ko suna zuwa asibitin suna kamuwa da ita. Idan mace ta hadu da ciwon kwakwalwarta ce kan juye tamkar na mahaukaci. Dan za ta yi ta surutai da hauka ba tare da ta san tana yi ba. Amma idan aka dage da magani za ta warke. Wasu kuma idan abin ya taba su sosai ko da sun warke rayuwarsu za ta canja ba kamar da ba, maganarsu da mu'amalarsu da kun gani za ku ce sun taba hauka". dakyar! ya tsahirta ganin wani tashin hankali da ya sake wanzuwa a fuskokin su ba kamar Mariya domin kukanta kara tsananta yayi cikim haka ta shiga kanƙame yaron dake hannunta sosai hawaye ke zuba a fuskarta. "Shikenan ta faru ta kare". abin da ta iya fadi kenan cikim hanzari ta mike daga durkushen da take ta nufi in da Ummanta take kwance cikin halin barci sosai dubanta take yi sosai kafin taja wani Numfashi mai karfi tana kara kanƙame yaron dake hannunta ta daga laɓɓanta dakyar domin jin kirjinta take yayi mata nauyi sosai kamar an dauko katon dutse an dora mata. "wai da gaske Ummata damuwa kika saka a ranki wai haka ne inji likita...". ta tsaya da maganar tana cizon laɓɓan bakinta na kasa tana mai nuna Dr. Aqeel kafin ta dora da cewa. "me yasa haka Umma mai yasa kika saka damuwa a ranki har hakan ta faru ina son ki sosai da sosai Ummata bana son abin da zai taba min rayuwarki don Allah ki tashi sannan ki ciwa likita kin cire damuwar da yace ki na saka wa a ran ki san hakan zai sanya wannan cutar da yace kina da ita zata bar ki bana son komai ya zamto da gaske bana so naji wannan DAYA BALA'I akan ki don Allah ki tashi ki fidda komai a rank...". "Mariyaa". Cak! ta tsaya da maganar ta ta jin muryar da ta ambaci sunanta cikin sauti mai dauke da kin abin da take fadi. "Ya haka Mariya ƙaddara ce hakan jarabawa ce daga Rabbi!". sosai ta juye ta na duban Dr.Aqeel sosai take jin sautin maganarsa na amsa kuwwa akanta sosai take jin za ta iya yin shiru ta amshi maganarsa amma ba tabbacin zuciyarta za ta iya amsa kau da kai tayi. Bello ne ya taso cike da sanyin jiki ya isa in da Mariya take ya janyota jikinsa yana bubbuga bayanta yana jin yarda zuciyarta ke harbawa sosai cikin sakanni yama jin yarda tausayinta ke ratsa masa zuciya sosai yake jin zafi a ransa game da wannan lamari. Sun jima cikin wannan hali tsayin lokaci ba wanda yayi kokarin yin magana a tsakani Dr.Aqeel yayi gyarar murya kafin yace, "ya kamata ace izuwa wannan lokaci kun gayyato natsuwa cikin duniyarku...". "Ya ya hakan zata kasance Likita". Sai lokacin Bello ya samu motsa laɓɓansa ya furta hakan. Sosai Dr.Aqeel yake dubansa musamman tashim hankalin da ya hango girke cikin idanuwansa ya sani dole su ji ba dadi dole si u ji wani iri a ransu musamman irin wannan lamarin da yake da wuyar gane akan wanda mai sansh ba ya sani dole su tsorata sosai da lamarin saboda ganin bakon abu ne a garesu. Sai dai abin da Dr.Aqeel bai sani ba abin da ke damun Bello shi lamarin Habeeba ya yarda za a bukaci kudi da ya san ba shi da su sam! a bangaren halin da Habeeba ke ciki ya sani komai daga Allah ne komai in ya faru da bawa muƙaddari ne to ya dauka komai ya faru da Habeeba Ƙaddararsu ce daga Rabbi! ba yarda za suyi zai sanya hammu bibbiya ya karba. "likita naji bayanin kumana gode, da wannan fahimtarwa da kayi akanmu mage da rashin lafiyar da Habeeba ke ciki sai dai kuma Uhmm...". Sai kuma yayi shiru ganin irin kallon da Dr.Aqeel ke yi masa mai dauke da murmushin karfafa guiwa ya nisa. "kar ka damu komai zai zo da sauki da yardar Allah". Gyada kai kawai yayi ba tare da ya sake cewa komai ba Dr.Aqeel ya mike yana mai duban Mariya dake takure waje guda sai ajiyar zuciya take kamar wacce tayi gudun ceton rai. "ki kula dashi sosai in ya tashi kafin na dawo ki sake bashi madararsa ga ruwa nan ma zaki iya bashi amma dai ya fi kyautatuwa ki bashi madarar kawai". gyada kai kawai take yi domin bata da karfin iya bude baki ta ce wani abu don ji take bakin nata yayi mata nauyi sosai da sosai. "Mun gode". Bello ya fadi lokacin da Dr.Aqeel ya juyo da kallon sa gareshi ya fara tafiya domin barin dakin. "zan dawo nan da minti talatin don Allah ku kula sosai komai kuka ya faru kuyi hanzarin nema na kafin lokacin dawowa ta". Daga nan bai sake cewa komai ba ya fice daga cikin dakin yana duban hannunsa mai daure da wani ratsattsan Agogo mai kalar whiter and Blue sosai Agogon ya dace da hannunsa mai cike da kwantacciyar suma baka mai dan haske sannu a hankali yake takunsa cike da natsuwa har ya karasa ficewa daga cikin dakin idanuwan Mariya na kansa sosai take son halin mutumin mai tattako lokaci guda taji yna burgeta domin taimakon da yayi mata ba ita kadai ba hatta mahaifinta DR. AQEEL MUNKA'IL ya burgeshi sosai da sosai. [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA TARA. Sosai ta shiga duniyar tunani tana kokawa dashi a yarda komai yake cakuɗe mata lokaci guda duk wata tufka da take yi ba a zuwa ko ina take wargajewa sosai take tunani wanda ita kanta bayi tsammanin kwakwalwarta zata iya yinsa ba ba tare da ta tarwatse ba hankalin ta sosai ya karkata zuwa ga duniyar tunaninta ta bar duniyar zahiri. Tafiya take sannu a hankali wanda ita a karan kanta ba ta ina take jefa kafa ba kamar daga sama taji wata irin kara gabadaya ta karaɗe mata kunnuwa cikin yanayi na tsananin firgice ta dawo duniyarta ta na faman ambaton Allah gabadaya ta daura hannu akai ta rasa ita a ina take a wannan lokacin domin ta gama yanke tsammani komai zai faru a lokacin ba mai dadin ji bane sam! cikin duniyarta sosai take jin sautin na sauka a hankali gabanta ya fara raguwa daga faduwa da yake yi a hankali ta fara kokarin buɗe idanuwanta da suke runtse sosai jikinta gabadaya sai karkarwa yake yi kamar wacce aka jonawa wayar wutar lantarki. "Ke!". Kamar daga sama ta ji wata muryar ta amsa amo ga kunnuwanta sosai taji tsawar a ranta sosai da sosai gabanta ya fadi dalilin tsawar a hankali ta daga kanta da idanuwanta da suka rine sukayi jajir sosai. Tsakiyar titi ta ganta tsaye ga wata bakar mota mai matukar dauka ido gabanta haske rana sai haske yake yi gefe guda kuwa wani matashi ne wanda ba zai hau shekaru ashirin da takwas ba zuwa talatin baki ne dogo mai kaurin jiki fuskarsa doguwa ce mai dauke da dogon hanci da manyan idanu masu kalar barci (sexy eyes) girarsa cike take da suma baka sidik da ita bakinsa dan madaidaici mai dauke da Laɓɓa Pink kala mai duhu kadan haka kansa akwai suma kwantacciya wanda ta samu gyara sosai tayi luf a samankansa sai faman kyalli take yi jikinsa sanye yake da kananun kaya farin wando jeas sai riga mai kalar Ash-colour a gaban rigar an yi rubutu kamar haka *SO MUCH LOVE YOU* da kalar ruwan Gold kafarsa kuwa takalmi mai kalar silifas mai ruwan kasa-kasa sosai da sosai takalmin ya amshi kamarsa mai dauke da dogayen yatsu wanda suka sha gyarar farata sosai. Lokacin da Mareeya ta gama ƙare masa kallo lokaci guda ta kau da kai gami da jan guntun tsaki kafik ta sake daga idanuwanta ta dube shi shima ita yake kallo wanda kallon ba za ka iya ajje shi a mataki daya ba ne tausayi ne ko na kiyayya Gefe da gefen titin kuwa tun da abin ya faru jama'a sukayi cirko-cirko suna kallon abin da zai wakana domin har ga Allah kowa ya sadakar mai Motar nan zai yi sama da Mariya sai dai buzunta amma sai Allah yayi ikonsa ko taba bai yi domin kuwa hanzari yayi sosai wajan taka burki. "ke wacce irin dakikiya ce baki da hankali ne na lura da alamun kan ki akwai ciwo a cikinsa ko". Sosai ya ke maganar cikin fada yana faman daga hannu kamar zai kwashe ta da mari yana kara fiddo da manyan idanuwansa waje yana sauke su akan ta ita har zuwa lokacin idanuwanta na kansa sai dai sun cika kwalla sosai kadan suke jira su zubo. Nisawa yayi bayan ya gama kare mata kallo sosai da sosai. "a fuska kamar mai natsuwa amma sam ba haka bane na lura ba ke burik rayuwar duniya cikin duniyar ki sam! bakya lale marhabin da duk wani farincikin duniyar nan a rayuwarki". sosai take jin sautin kalaman sa na sauka a kunnuwant suna samun masauki sosai take jin daci da bauri a kalamansa sosai take jin ranta yana baci da sauri ta kau da kai daga barin kallonsa bayan ta watsa masa wani kallo wanda a karan kanta ba ta san tayi sa ba. "In ba ki son Rayuwar duniyar ai gwanda kawai ki fadi ki samu wani ya turmushe ki da mota ko ya gille maki makoshi da wuka ba wai ki zo ki daura mani zunubin da ba nawa ba haka kawai ban san hawa ba sai naji sauka ki jaza mani BALA'I ki bar ni da zaman gidan kaso". Ta fara gajiya da kalamansa sosai komai take ji nata yana jin haushinsa sosai take jin bakin cikin haduwa dashi a wannam lokacin. "ga ki Mace har mace amma bakin san dadin rayuwar 'ya mace a duniyar nan ba na lura CUTA KAI ki ke dashi kuma bakin DARAJAR dakike da ita ba da kinsan DARAJAR 'YA MACE a duniyar nan wallahi ba zaki so mutuwa ba". A firgice ta dago idanuwanta wanda a wannan lokaci suka fra zubar hawaye ta sauke akansa mamaki ne ya cika mata kwanya sosai a zuciyarta ba abin da take ayya nawa illa anya mutumin nan na da hankali kuwa anya bashi ya dace alakabawa kalmar hauka ba anya bashi ya cancanci a kira mai CUTAR KAI ba anya bashi kansa ke ciwo ba... "In da ni ce ke wallahi ko hanya da ganganci da BALA'I yake ba zan bi ba ke Tsautsayi in da ana ganinsa billahillazi ba zan doshi in da zai doso ni ba har ya shigo rayuwa ta ba". Ta gaji tayi matukar gajiya da jin maganganunsa komai taji nasa ya bata mata rai sosai ba za ta iya tsayawa ta saurare shi ba abin sai yayi yawa da wanne za ta ji da halin da ƘADDARA ta je fata ko kuma da wannan banzayen kalaman nasa da taji masu kokarin haifar da CIWON RAI. "Malama yasin ki ceci rayuwarki don duniyar nan gidan zamana gidan kuma jindadi...". Ba jira ya dora a zancen sa ba ta mike ta fara tafiya a hargitse kamar wacce ta samu tabin hankali tafiya kawai take yi domin ji take yi kalaman wannan mutumin na koƙarin hauka ta mata hankalinta sosai da sosai hannu ta saka ta rufe kunnuwanta domin bata bukatar ta sake jin ko kalma daya ne daga cikin kalamansa ba ta so ko ganinsa ta sake yi ko a badininta domin ta sani Mummunar ƙaddara ce ta jeho shi rayuwarta ba komai ba domin kalamansa sun gama tabbatar mata da halinsa ta lura duniya gabadaya ta gama daureshi tamau har da rararr igiya. Tafiya tayi sosai mai nisa daga bakin titi sosai take tunani tana faman sharce gumin da yake karyo mata dayake lokaci ne na rana ba wai zafin ranar bace ta dame ta a,a wannan mummunar gamon da tayi ne gabadaya ya kara jagula mata lisssafin ta sosai take jin takaicin fitowarta sosai take jin haushin wanna rana sosai zuciyarta da ruhinta suke zafi komai yana kara lalace mata. "Yaa Rabbi!". Abin da laɓɓanta suka kokarta fadi kenan cikin wani irin yanayi mai dauke da tashin hankali sosai. Sannu a hankali ta isa gida kafin ta shiga sai da ta tsaya bakin kofa kamar mai kokarin tunano wani abu kafin ta ja dogon numfashi ta doshi cikin gidan baki ta dauke da Sallama tun daga soro ta fara jin rashim mutane a cikin gidan sosai da sosai take jin shiru ya gauraye gidan ba motsin ko dan tsako a cikin sa a haka har ta isa tsakar gidan ta tsaya yana a yarda suka barshi ko alfarmar shara bai ci ba gyada kai tayi kafinta doshi dakin mahaifiyarta. Sosai take jin tausayin kanta sosai komai ke dawo mata sabo sosai take tuna ranar sosai take tuna komai sosai take tuna mahaifiyarta da komai da ya faru da ita can baya sosai da sosai taji zuciyarta na kara rauni ruhinta taji yana kokarin ajje mata komai kamar yanzu ya faru. Kuka ne yake kokarin kwace mata wanda ita kanta ba ta san ya akayi ya zo ba ko da yake bai dace tayi wa kanta wannan tambayar ba domin ta sani ABOTA suka kulla dashi wacce ba ta tsammani akwai ranar yankewar ABOTAR. hannunta duk biyu ta saka ta rufe bakinta domin ji tayi kukan na kokarin ba da sauti sosai da sosai. Da sauri ta mike tashiga neman abin da ta zo dauka cikin lokaci ta kammala komai ta hada ta dauka komai tana yinsa ne cikin rashin hayyaci domin ta tabbata in ta zauna cikin dakin nan zuciyarta za ta iya bugawa ba za iya zaman sa ita kadai ba bata so ba za ta iya ba Allah ya gani gabadaya gidan ne ba ta son zaman sa a wannan lokaci ba za ta so ace ta zauka ba domin DUHU take gani sosau wanda yake kokari rufe mata idanuwa har ma da zuciya da ruhi a hanzarce ta bar dakin cikin sakanni ta bar cikin gidan gabadaya har zuwa lokacin hannayenta na rufe da bakinta domin bata bukatar kukan ya fasu. gabadaya hankalinta ya tafi fatan ta ace ta ganta a cikin dakin dakin da mahaifiyarta take tare da mahaifinta ba ta so ace tayi nesa da su bata so ace komai ya fau bata nan tana so ace komai in ya tashi faru ya faru akan idon ta ta shirya ta shirya sosai da sosai komai za ta iya dauka komai da zai faru ta shirya masa zata iya jurewa za ta yi dauka ko meye ma ta shirya masa... "MACE ƘYANƘYAWA". 'Innalillahi wa'inna ilaihir raji'una' Mariya ta dankara cikin tashin hankali domin wata katanga ce ta ji ta ruguzoma mata mai dauke da bama-baman tashin hankali sosai taji duniyar na juya mata sosai take ganin wasu taurari masu dauke da kayan yankin kawo mata tashin hankali na shawagi a idanuwanta ba ta san lokacin da ta zubda kayan dake hannunta ba ta daura hannu saman kai tana kokarin kurma ihu amma kafin ta kai ga aikatawa taji wani lallausar hannu yayi wa bakinta ƙawanya habawa ai Mariya ji tayi kamar taji ta ta nutse cikin kasa sosai taji jikinta gabadaya ya tsaya cak! duk sani abu mai rai da motsi na jikinta sai da taji yayi mutuwar wucin gadi zuciyarta kuwa ji tayi kamar ta tarwatse tayi daidai sosai komai ya fara dawo mata jikinta ya dau mazari idanuwanta a rintse sosai. sautin ajje murmushin sa taji ya dakar mata dodan kunni kafin taji sautin muryarsa. "Anya kuwa na dauka zan ganki a jaruma lamba guda amma sai na ga akasin haka". sosai ta sake runtse idanu gami da sanya hannayenta ta toshe kunnuwanta ba abin da take ambato sai Allah a ranta da ruhi. "Don Allah". Ta fadi cikin tashin hankali da rashin abin yi Sosai yake kallonta da yanayin da ta firgice lokaci guda gabadaya idanuwansa ya juye akanta yayi mata kur! da idanu fuskarta yake kallo bakinta dake rawa yake kallo sosai da yarda ta motsa laɓɓanta ha ta furta 'Don Allah'. "Me nayi miki?". a dan tsorace ta bude idanuwanta ta kalle shi ta sauke da sauri domin ba tayi tsammanin idanuwansa na kanta ba. "Kayi Hakuri...Don Allah". Miƙar da ita yayi daga durkushen da tayi sosai yake kallonta yana kallon yarda jikinta ke rawa da alamun tsoro sosai take ji akanta murmushi ya saki kafin ya motsa laɓɓansa. "Ba abin da kikayi mani, ki natsu mana garki ba da mata mana". Ba ta son jin muryarsa balle kuma kalamansa wanda take yi wa kallo a yan ta'adda da fashi da makami domin ba komai cikin kalaman nasa sai kokarin kashe rayuwar wani rai. "Ya sunanki?". Ya fadi a wannan lokacin yayi kasa sosai da muryarsa cikin rarrashi. ta gefen ido ta kalle shi har yanzu idanuwansa na kanta a dam tsorace ta waje idanun nata sosai tana motsi da baki alamun son magana da kyar ta samu ta furta. "Mariya". A nata tunanin in ta fadi zai sake ta domin rikon da yayi wa hannunta ji take yi kamar wuta domin haushi da takaici gabadaya ya rufe ga kuma tsoransa da take ji ya samu waje a zuciyarta ba ta so ƙaddara ta sake watso mata shi a rayuwa ba ta lura ƙaddara sam! ba ta son ta in dai a faggen natsuwar rayuwarta ne. Sosai taci dacin abin da yayi mata ya taso mata cikin karfin hali ta dago kai ta watsa masa wani kallo mai cike da gargaɗi kafin ta fara motsa laɓɓanta. "Meye hadi na da kai na dauka tun dazu muka raba gari da kai ko? to don haka ka rabu dani ka fice daga duniyar rayuwata ba abin da ya gama ka dani ina mai rokon ka ka tafi". Tun da ta fara magana yake kallonta yana sakin wani irin Murmushi wanda ya dan tsorata ta amma ba ta bari hakan yayi tasiri a zahirin fuskar taba kau da kai tayi gami da jan guntun tsaki. Lokaci guda murmushin dake kan fuskarsa ya dauke sosai ya ji zafin tsakin da yaji tayi masa yarinya karama har ta kalli tsabar idanuwansa tayi masa tsaki sosai yaji abin a ransa amma sai ya kanne ya sake gayyato murmushi ya daura a fuskarsa. "MARIYA". ya ambaci sunan cikin amo mai sauti ita kanta sai da taji faduwar gaba duk da taji wani iri da yanayin da ya ambaci sunan nata kamar shi ne ya halicce shi. Ba tanka ba kamar yarda shima baya bukatar haka. "HUZAIF". ya fadi yana mai haɗe laɓɓansa waje daya yana cizawa sosai yake jin daci a ransa sosai da sosai yake jin bakin cikin abin da yarinyar nan tayi masa ba ya tunanin a duniyar rayuwarsa akwai 'ya mace mai amsa suna mace ta taba kallonsa tayi masa haka ko a cikin mafarkinsa gyada kai yayi. "Bani da wata niyya akan ki ta cutar wa ki yarda dani in da ni mai cutarwa ne da tuni komai ya tabbata akan ki na cutarwa". Sosai yayi kasa da muryarsa ya na furucin yana kallonta ita kuwa kanta na kasa gabanta na faman bugawa duk sakan sosai take jin tsoro da firgice na mamaye ilahirin jikinta zuciyarta tana amsa amo da sunan da taji ya ambata. Ba ya zata yarda dashi ba ko kadan, domin dukan farko da yayi mata shi ya tabbatar mata da ko shi waye, don haka dole ta nemi tsari dashi a duniyar rayuwarta da sauri ta durkusa tashiga hada kayanta da suka warwatse bayaj ta fizge hannunta daga gareshi ba ta sake bi ta kanshi ba komai yin sa take cikik hanzari da kokarin barin wajan domin ba zaiya cigaba da tsayu dashi ba ko kadan ba ta muradin hakan. Huzaif mamaki ne ya cika msa zuciya sosai yarda da ya ga Mariya na komai nata cikin nuna halin ko in kula gareshi ya lura sosai cikin idanuwanta akwai tsanarsa hakan ba karamin mamaki ya bashi ba saboda bai san dalili ba shi dai ya san bai yi mata wani abu na cutarwa ba amma yana mamakin yar da tsanarsa ta sami gurbin zama a kwayar idanuwanta wanda ya tabbatar hakan ne har a zuciyarta. Murmushi ya saki gami da dunkule hannayensa waje guda ya zuba mata idanu yana kallon yarda take tafiya cikin sauri saurin da daka kalle shi ba jarumta a cikinsa domin tafiya take tana hada hanya kamar wacce tayi tatir da kayan maye. Sosai Mariya take ji a jikin ta ana kallonta tun da tabar wajan domin tasan dole hakan ta faru dama sosai zuciyarta ta shiga saƙar fargaba domin sosai take jin tsoron Huzaif ko da dai bai nuna mata a kalamansa ba amma ta ji a jikinta haushin ta yake ji haushi na sosai da sosai. Sai da tayi nisa sosai sannan ta ja burki ta tsaya tana mai da numfashi har zuwa lokacin kuma jikinta bai bar sanar da ita ana kallonta ba. A hankali ta juya sosai gabanta ya yanke ya fadi domin hango shi tayi zaune saman Motarsa mai kirar BMW M6 baka wuluk da ita idanuwansa na kanta da sauri ta dauke kai tana mai ambatar. "Yaa Rabbi! Kayi min tsari da wannan mutumin da yake kokarin bibiyar rayuwata". Kara azama tayi a tafiyar ta sosai take sauri kamar wacce zata kifa kallo daya zaƙayi mata ka tabbatar da ba natsuwa game da ita duk in da ta gilma sai an bi ta da kallo domin kuwa gabadaya a hargitse take daurin zanin da yake jikinta abin a kalla ace ba natsuwa ne haɓa daya ta zanin sai faman reto yake yi yana jan kasa kafar nan ta ta bututu tayi da jar kasar dake hanyar da take bi zuwa komawa Asibitin. Tunda ta bacewa ganinsa ya koma cikin Motar sa ya yi mata Key ya bi bayan ta a hankali har ya isa Asibitin shi ma can gefe guda ya samu yayi Parking ya fito yana karewa Asibitin kallo tunda daga zubin yanayin Asibitin da tsarinsa ya tabbatar sai marasa hali ne masu zuwa cikinsa don shi dai ya tabbata ko mura yake yi ba zai zo wannan asibitin da sunan neman magani ba sosai ya shiga tunanin abin da ya kawo Mariya wannan Asibitin ya tabbatarwa zuciyarta kila wani nata ne bashi da lafiya lura da yayi da yanayin datake ciki ya tabbata nata ne makusancin na sosai da sosai ba lafiya ji yayi kamar ya shiga asibitin amma sai wat zuciyar ta hanashi tana mai tambayarsa in ya shiga yayi me? A matsayin sa na wa zai je gareta? Tambayoyin da suka taru akansa kenan ya fasa shiga asibitin da sauri ya juya ya fada motarsa ya ja ta ya bar bakin Asibitin. Da shigar Mariya Asibitin ba in da ta dosa sai dakin da Mahaifiyar ta take a kofa ta tadda Mahaifin nata zaune ya zabga tagumi sosai ya shiga damuwa sosai za ka fahimci yana cikin yanayi matsananci. "Baaba!". Mariya ta fadi cikin sauti da rauni a muryarta kamar zata rushe da kuka. A hankali ya dago idanuwansa da sukayi matukar canza launi sosai tashin hankali ke zagaye da su. "Har kin dawo Mariya?". ya fadi cikin sanyin murya. Gyada kai tayi gami da samun waje kusa dashi ta zauna tana ajje numfashi da kyar. Ba wanda ya sake kokarin tankawa a tsakaninsu tsayin lokaci suna cikin halin shiru kafin Mariya ta nisa cikin sanyin jiki. "Uhmm amma Baba ya na ganka a nan zaune wa aka bari da Umma?". Ta tambaya tana mai kafeshi da idanuwanta da suke a hargitse. Shiru yayi ba tare da ya bata amsa ba har ta fara tsire tsammani da amsawar tana kokarin sake magana taga ya motsa laɓɓansa. "Barci take yi". "Har yanzu bata tashi ba?". Ta sake tambayarta domin lokacin da ta bar asibitin a cikin halin barci ta bar ta. "Ta farka ta sake komawa". Mariya ta fara motsa laɓɓanta ta na son yin magana sai ga Dr.Aqeel yayi Sallama garesu amsawa sukayi Mariya tayi masa Sannu da zuwa. Murmushi yayi kafin ya ce, "Mariya har kin dawo kenan. na zo dazun Abban ki ke cewa dani kin je gida". Gyada kai tayi gami da kalato Yaƙe ta ajje a fuskarta. Shiru ne ya tsake ziyartar wajan ba wanda ya sake magana sai ajiyar zuciyoyi dake fiddo da sauti sosai lokaci yaja a tsakanin su har zuwa lokacin ba wanda yake kokarin tsinkawa. Dr.Aqeel da ke tsaya hannunsa rike da wani File yana dubawa bayan ya gama ya dube su. "Hala ciki da zafi kuka zauna a nan?". "Ko daya Likita kawai gani nayi tana barci na fito nan na zauna". Gyaɗa kai kawai yayi bai sake magana ba ya juya bayan yayi musu sallama ya tafi. Mariya ta bishi da kallo sosai halin Dr.Aqeel ke burgeta natsuwarsa gami da karamcin sa yana kara mata mutuncinsa a idanunta sosai take ganin girmansa tabbas ta yarda ba duk mutane bane suke iri daya a duniyar nan ta yarda halintar Dan-adam daya ne amma halin kowanne ya bambanta ba ta taba tsammanin za su samu mutum mai karamci da taimako irin Dr.Aqeel a da can ta dauka kowa ba mai kirki bane ashe da bambanci. "Amma Mariya naga kin jima kafin ki dawo ina kika tsaya?". Bello ne ya katse mata tunanin zuccin da take yi da sauri ta dube shi tana faman gyada kai sosai ya kafe ta da idanu ganin halin da ta nuna hakan ya kara daburta mata tunani ta rasa amsar da zata baiwa mahaifin nata shin ta fada masa haduwarta da mutumin da ya kusan kashe ta tun lokacin ta bai yi ko kuwa... "Kika yi shiru?". Ya katse mata tunanin da ta afka. "Uhmm dama ba abin da ya tsaida ni kawai dai wani ne...". Sai kuma tayi shiru ta kasa krasaw domin yanayin da ta ga Mahaifin nata ya nuna sai tayi da nasanin sakin bakin da ta so yi domin ta san tabbas sai ya ji ba dadi in har ta fada masa. "Wani mutum yayi me?". Ya fada ya na kafe ta da idanu sosai hakan ya sanya ta shan jinin jikinta a dan daburce ta daga laɓɓatanta. "Bakomai". Shiru yayi yana nazarin maganar tata ya tabbata akwai wani abu amma da alamun ta na tsoron sanar dashi. "Allah ya kyauta". Abin da ya fadi kenan ya koma ya zabga tagumi. 'Ameen' Mariya ta amsa ita ma a ranta gami da mikewa domin kai kayan da ta zo da su cikin dakin. [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA GOMA. Dr.Aqeel zaune cikin Office din sa gabadaya hankalinsa ya ta'allaka ga File din dake gabanda yana dubawa tsayin lokaci ya shafe a haka lokaci-lokaci yana sanya biro a bakin sa yana cizawa kamar son samu wata amsa daga gareshi. Kamar dag sama yaji ana knocking din kofarsa a hankali ya daga kai ya kalli kofar na yan dakiku kafin ya mai da File din ya rufe ya ajje shi gefe sannan ya motsa laɓɓansa. "Yes Come in". ya kafe kofar da ido yana jiran ya ga waye zai shigo sai da aka shafe yan sakanni kafin sautin murɗa kofar ya fara kaiwa kunnuwan Dr.Aqeel sako sosai yake kallon kofar har ta gama bude wani matashi me ya bayyana fuskarsa ba yabo ba fallasa ya shiga takowa har ya iso gaban Table din Dr.Aqeel tun da ya shigo yake bin sa da kallo kallon kamar na san ka amma na kasa tuna baya. "Dr.Aqeel Munka'il". ya fadi yana kokarin zama kan daya daga kujerun dake girki kusa da table din fuskarsa dauke da murmushi. Sosai Dr.Aqeel yake kallon sa shi ma yana sakar masa murmushin yaƙe. "Dr.Hisham Muktar Karami". Wata irin zabura Dr.Aqeel yayi yana mai zaro idanuwa gami da sakin wata yan kara kadan. "OH My God! Da gaske kake wai ko wasa ko a tunani ban kawo hakan ba". ya fadi yana mai hanzarin baro in da yake zaune ya iso gareshi gami da kai masa wata irin runguma sosai suka sarke a junansu fuskokinsu dauke da murmushi da jin dadi da farinciki sosai sun jima haka kafin su saki juna har zuwa lokacin idanuwan Dr.Aqeel su na kan Dr.Hisham sosai yake kallon sa gani yake yi kamar ba shi ba. "Please Zauna mana Dr.Hisham ashe rai kan ga rai a duniyar nan ko a mafarki ban yi tunanin zan sake ganin ka ba". ya karaeshi yana kokarin isa wajan karamin firij din dake girke a can gefe. "Hmm Dr.Aqeel kenan ka yada zumunci shiyasa sam ka man ce da in da nake". shima ya fadi yana dariya yana bin cikin Office din da kallo yana mai murmushi sosai da sosai ya burge shi musamman tsayin da akayi masa komai nashi tsaf-tsaf dashi. "Yaa Allah! stop saying wannan maganar ma cos ba ta dace ba sam ka fade ta kai kanka ka sani ba haka nake ba". Dr.Aqeel ya fadi yana mai murɗe murfin robar Ruwan EVA mai rangwamin sanyi ya tuntula cikin glass cup din dake aje. "Bismillah". ba musu ya dauka ya kai bakin sa sai da yayi rabon cup din sannan ya ajje gami da ajiyar zuciya fuskarsa da murmushi yake kallon Dr.Aqeel wanda shima idanuwansa na kan sa. "ka canza gabadaya kamar ba kai ga kayi kiba ga wani tumbi da aka ajje". ya fadi yana mai kyalkyalar dariya " ni da kai waye yafi zama kato ka dube ka fa Dr.Aqeel". "Five years is not 2years fa wallahi". Dr.Aqeel ya fadi yana mai harararsa cikin sigar wasa kafin dakin ya dau shiru na dan lokaci. "gaskiya kam! na yarda tun da gashi nan nagani har ka kasa gane ni da alamun nan da shekara goma in ba ka ganni ba ko nace ni ne Dr.Karami ba zaka yarda ba". "No ba haka bane wallahi, yanzu dai yakake ya kuma aiki ya bayan rabuwa?". "Alhamdulillah mun godewa Allah kasan yanzu ina can Delhi ne acan nake aiki da wani Privter Hospital". "Ba Shakka ka ji manya mu ku ga mu nan muna ta fama da asibitocin nakasarmu". Murmushi Dr.Karami yayi kafin yace. "nikam narasa abin da ke damun kasar tamu har yanzu jiya-i-yau ba abin da cigaba na a zo a gani da aka samu". "Uhmm kai dai ayi sha'ani kawai Dr.Karami". Sosai Dr.Karami ya kafe shi da ido kamar mai nazarin wani abu kafin ya murmusa. "Ina Family?". Ya fadi yana kafe shi da idanuwa. Murmushi yayi shima yana gyaɗa kai. "Har yanzu...". "Ban yarda ba". Da sauri ya tare shi. "seriuos". Shima ya fadi yana murmushi Sosai Dr.Karami yake kallonsa kamar wanda bai yarda da abin da yace ba ko daya ke ba zai yi mamaki ba in ya yi la'akari da kansa wamda shima ko dam tsako bai ajje ba. "Anya kuwa Dr.Aqeel kana nufin har zuwa wannan lokacin kai ma bakayi aure ba?". Sosai Dr.Aqeel yake kallonsa yana nazarin maganarsa da yarda yake danganta kansa da maganarsa. "kana nufin kai ma baka yi ba kenan?". Gyaɗa kai yayi yana murmushin yake. Kofar da aka banko ne ya sanya su saurin duban kofar Mariya ce ta shigo a hargitse sam ba ta lura da ko su waye a cikin office din ba idanunwanta gabadaya sun rikice bakin ta ba abin da yake ambata sai sunan Dr.Aqeel. Duk kan su ido suka zuba mata suna kallonta sosai cike ganin tashin hankali cikin idanunwata da gangar jikinta sosai suke kallon yarda jikinta ke ƙarƙarwa kamar wacce aka tsamo daga kogi Dr.Aqeel ya mike da sauri domin shi yasan komai akan Mariya rike yayi sosai da hannunsa yana faman kiranta amma ina tashin hankalin da take ciki duk ya tafi da yan guntuwar natsuwarta. "Yaa Allah Mariya me kuma ya faru ne?". Sai a lokacin ta lura da Dr.Aqeel da ke rike da ita sosai take kallonsa idanuwanta sai faman zubda kwalla suke bakin ta na rawa tana faman ajje zuciya. "Ummata Dr. Don Allah...". Sai ta rushe da kuka sosai hakan ya kara rikita Dr.Aqeel da sauri ya fara kokarin jan hannunta. "Dr. Aqeel What is wrong with her?". Dr.Karami ya fadi yana mikewa tsaya ya fara takowa har ya iso gabansu sosai yake kallon Mariya tun daga yatsun kafarta har izuwa cikin kwayar idanuwanta da sauri ya kau da kansa ya mai da idanuwan ga Dr.Aqeel. "Tell me now Please what is wrong with her". ajje Numfashi Dr.Aqeel yayi kafin ya dubi Mariya sosai yaji tausayinta na kara samun mazauni azuciyarsa. "Dr.Karami wallahi mahaifiyarta ne ke cikin Matsala". Da sauri Dr.Karami ya dubi Mariya wacce a lokacin ta tsagaita da firgicin da take yi na tashin hankali sai faman ajje numfashi take kamar wacce tayi gudun famfalaƙi sosai yake kallonta wasu abubuwa ne wanda bai dan ina suka dosa ba suke sukuwa cikin zuciyarsa sosai yake jin tausayinta a zuciyarsa tun kafin yasan abin da yake dawainiya da duniyar rayuwarta ita da mahaifiyarta yarinya ce karama wacce ba zata haura shekaru sha biyar ba amma yanayin ta ya nuna tana cikin MATSALAR RAYUWA ba kadan ba daga yanayin ta zaka gane haka. "Meke damun mahaifiyar ta ta?". Dr.Karami ya fadi yana sauke idanuwansa kan Dr.Aqeel. "eclampsia take fama dashi wallahi haihuwa tayi to tun bayan haihuwan lamarin ya afku". Gyaɗa kai ya shiga yi yanayin fuskarsa na sauyawa sosai da sosai tausayi da jin ƙai duk suka kara bayyana sosai. "Tana ina yanzu haka?". "Tana cikin Asibitin nan a kwance yau kimanin sati uku kenan da faruwar abin amma lamarin sai a hankali nayi iya bakin kokarina amma abun ya ci tura domin abin kara hauhawa yake yi". "Yaa Allah!". Dr.Karami ya fadi yana mai dafe kansa sosai yaji wani iri a game da abin da Dr.Aqeel yace dashi sosai yaji yana son ganin matar yana ji a ransa zai iya taimaka mata domin kuwa yana cikin fannonin da yake aiki akai. "Muje na ganta". Abin da yace kenan ya fara taku yana kokarin ficewa daga Office din kamar ya san in da dakin mara lafiyar yake da sauri Dr.qeel yaja hannun Mariya suka bi bayansa sannu a hankali har suka isa dakin da Habeeba take suna shiga suka tadda ita tayi firgai-firgai da ita alamun ya nuna duk ta hargitsa kanta amma izuwa wannan lokacin tayi lakwas ta hada jikinta waje guda ta saka laɓɓanta cikin baki sai faman cizawa take yi da sauri Dr.Karami ya isa gareta hannunta ya kamo gami da sauri ta fizge ba tare da ta kalleshi ba ya sake kai hannunsa ya kamo hannunta nan mata ta shiga kokarin fizgewa amma rikon da yayi mata a wannan karon bana wasa bane hakan bai bata damar kwace kanta ba illa dago idanuwanta da tayi ta watsa masa su sosai ya shiga karantar komai nata tsayin wasu dakiƙu kafin ya sake ta ya dubi Dr.Aqeel da Mariya da suke tsaya suna kallon duk abin da yake yi. "yanayin ta ya nuna abun yayi karfi sosai a gareta wanda hakan ya kusan zame mata tamkar hauka ta gaskiya ya kamata ace ta samu kulawa sosai da sosai a wannan matakin". Dr.Karami ya fadi Dr.Aqeel ya ja numfashi. "ka ga dai yanayin asibitin namu Dr.Karami ba komai bane ake samu a cikin sa wai don ma ina cikin sa ne ka gan sa a haka nayi iya bakin kokari akanta amma abin ya so ya faskara". Gyaɗa kai yayi cikin yanayi na gamsu da maganarsa ya san Dr.Aqeel gwani ne kuma jarumi ba zai ga gazawarsa ba a fannin aikinsa domin yasan kwarewarsa akan aikinsa sai dai matsalar da ya fara lura da ita a nan ita ce rashin kulawa daga gwamnati da kuma rashin wadatartun kayan aiki da babu dole duk wani likita ya fuskanci kalubale sosai a fannin aikinsa in har asibitin da yake ba kayan aiki numfasa yayi a ransa yace, 'dadin kasashen waje kenan kumin kankantar Asibiti ba zaka rasashi da kayan aiki ba amma ban da kasarmu ta najeriya komai na su sai ka ga ragwanci a ciki'. Amma a zahiri sai yace, "Shikenan Dr.Aqeel ina son wannan lamarin ya dawo hannu na nayi maka alkawari nan da KWANA SITTIN in Allah ya yarda zan yi iyakar bakin kokari na don ganin komai ya zama Normal". Dr.Aqeel yayi shiru yana kallon sa yasan ALHERI irin na Dr.Karami tun suna tare acan kasan America ya san shi farin sani mai taimako da jin kai ba wannan bane karo na farko da yake taimaka masa a aikinsa sosai yaji dadin abin da yayi masa fuskarsa da murmushi ya dube shi. "Anya za ayi haka daga zuwan ka Dr.Karami zaka daukarwa kan ka aiki ko hutawa baka yi ba please leave it I'll do my Best to Help her...". "Please Dr.Aqeel stop saying that, ka bar ni kawai nayi, ai ni nace naji na gani ko, sai dai ban sani ba ladar ce kila baka so na samu kaso na nima". ya karashe yana mai murmusawa alamun joking cikin maganarsa. Shi ma Murmushi yayi masa gami da gyaɗa kai. "But at Now zan je gida na huta kafin zuwa gobe na zo domin gudanar da komai". "Bakomai Dr.Karami ko sati kace zakayi ai ba zan haka wannan damar ba". Duk kan su sukayi dariya gami da yin musabaha. Mariya tun lokacin da suka iso cikin asibitin ta ke gefe tayi musu kuri da idanuwa tana jin maganganunsa sai dai wani lokacin ba ta jin turancin da suke jafawa cikin zancen nasu sosai take mamaki musamman ganin Dr.Karami da yarda lokaci guda ba tare da sanayya a tsakani ba ya bada lokacin sa har yake ikirarin taimakawa mahaifiyarta tabbas na Allah ba sa karewa a duniya nan ba ta taba zaton zata samu mutane masu imani irin haka ba wanda za su ji kansu ba tare da sun san su suwaye ba tabbas ta kara gasgata maganar mahaifinta akan DAN-ADAM ba duk bane halayen su daya suffa ce kawai ta kasance iri daya ba ta dan lokain da wani guntun murmushi ya suɓuce mata ba mai dauke da hawaye hannu ta saka tana dauke su a daidai lokacin Dr.Karami ya sauke ganinsa akanta sosai ya kureta da idanu yana kallo kamar wanda ya ga wata sabuwar halitta sosai Mariya ta kaɗu da irin kallon da ta ga yana yi mata da sauri tayi kasa da kanta gabanta na bugun uku-uku ba kadan ba ta tsorata da kallon da yake mata ta shiga nazarin dalilin kallon nashi akan me yake mata kallo ko ya san ta ne a ina? da sauri ta girgiza kai domin bata tsammanin ya taba ganin mai kalar hauka irin ta firgitacciya sosai ta saka a ranta daga ganinsa dan kasar waje ba dan najeriya bane domin irin yanayin da ta ganshi fes-fes kuma muryarsa bata fita sosai kamar na Dr.Aqeel haka ya kara tabbatar mata kila ba bahaushe bane "Excuse me. whats is you Name?". Ya fadi yana murmushi a fuskarsa gabanta taji ya fadi domin ta tabbat da ita yake magana abu daya ta fahimta a maganarsa wato tambayar da yayi mata sunanta wannan kalmar tambayar kuwa ta ji ma da haddace ta a kwakwalwarta domin tun tana Primary ta san abin da furucin ke nufi a hankali ta dago ta kalle shi sannan ta kalli Dr.Aqeel wanda shi ita yake kallo da alamun jiran abin da zata ce yake yi domin irin kureta da yayi da ido amma da murmushi a fuskarsa a hankali ta motsa Laɓɓanta. "Mariya". Dr.Aqeel da ya yi kasaƙe da baki sai gashi ya zaro ido mamaki da al'ajabi ya cika shi da yaji ta ambaci sunata da alamun ta fahimci abin da Dr.Karami ya tambayeta sosai ya shiga tambayarsa kansa yarda akayi har ta iya bada amsa sam bai yi tunanin za ta iya ba bai yi tunanin ma ta taba shiga aji da sunan daukar karatu ba ganin yanayinta mamaki ya hana shi sakat har sai da ya dubi Mariya yace, "dama kin iya turanci ne dama kina makaranta ne?". Sai ta taji wani iri a ranta ji irin tambayar da yayi mata wato kallon BAGIDAJIYA yake yi mata ma rashin ilimi dakikaya yar kauye sosai taji ranta ya sosu wato shi tunanin sa saboda rashin babun sa yana tunani ya hanata shiga aji har ta nemi ilimi gyada kai kawai tayi gami da kau da idanuwanta daga gareshi gabadaya ta mai hankalinta wajan kaninta dake kwance yana faman barci cikin kwanciyar hankali yaron da aka yiwa Huɗubar suna Ibrahim wanda suke kira Mu'azzam cikin asibiti saboda tashin hankali da suke ciki... "kiyi magana mana". Dr.Karami ya fadi ganin ba ta da niyyar cewa komai kallonsa tayi a hankali ganin murmushi a fuskarsa wanda ta lura kamar hakan a jininsa yake yawan fara'a wanda hakan ke kara masa kyau matuka gaya. "Eh ina makaranta aji na biyu a sakandiri...". "A haka din?". Dr.Aqeel yayi hanzarin katse ta da fadin haka yana nuna ta da hannu cikin alamu da mamaki sosai a ransa. "Masha Allah!". Abin da Dr.Karami yace kenan ya kastewa Dr.Aqeel hanzarinsa ta hanyar cewa su tafi sai da suka sake duba Habeeba wacce a wannan lokacin ta daina komau da take yi har da cizon laɓɓanta a tausaye sukayi wa Mariya Sallama suka bar cikin dakin. Ajiyar numfashi Mariya ta saki gami da zamewa ta zauna kasa kamar wata kayan wanki ta zabga tagumi hannu bibbiyu tana faman kallon mahaifiyarta da kaninta Mu'azzam a wani sashin na zuciyarta kuwa Dr.Karami ne da Dr.Aqeel tana ji ba dadi akan yanayin da Dr.Aqeel ya nuna akanta yarda ya nuna yana mamaki da tace masa tana makaranta me yake nufi da yanayin da ya nuna kenan yana nufin 'ya'yan talakawa marasa galihu basa makaranta ne ko mi yana zaton rashin 'yancin 'ya'yan talakawa har ya kai suka sa yin makaranta su zauna cikin duhun jahilci to tabbas yayi kuskure in har haka tunaninsa ya bashi bai san masu son yin karatu ba bai son masu burin yin karatu a duniyar 'ya'yan takalawa ma naso sai dai babu ita ce take zame musu katanga da karatu. Haka Mariya ta zauna tayi ta zancen zuci har zuwa wani lokaci. ****** Dr.Karami cikin Motarsa Kirar 2019 Mercedes-Benz GLA yake tuki bayan ya baro Asibitin Baban Alis tafiya mai dan tsayi yayi kafin ya isa cikin garin Minna Unguwa Tunga daidai wani katafaren Get ya yada zango Horn daya yayi aka buɗe masa ya shiga tsararren gida ne sosai wanda ya ƙawatu da komai na adon gida ba abin da babu aciki can nesa kadan wajan Parking Space ya nufa ya ajje motarsa ya fito hannusa rike da wayarsa sai faman latsa ta yake yi da alamun kira zai yi kafin ya isa kofar da zata sa dashi da Falon gidan ya kai wayar kunnansa sakan ni kadan ya fara magana. "Am so Sorry Engr.Dangi wallahi lokacin da ka kira ni ina driver ne shiyasa ban dauka ba But Now na dawo gida dafatan dai lafiya?". Ya karashe maganar tasa da dora tambaya. Daga can dayan barin yaji sautin murmushi ya tashi kafin ace dashi. "Albishirinka". "Goro fari tas". ya fadi cikin sauri domin tun da yaji Engr.Dangi yayi irin wannan zancen yasan akwai kayan farinciki da suka wanzu kenan. "Kayi Kani Dr.Karami". "seriuos don Allah Engr. Dangi ban son joking irin naka wallahi tell me the True Please". Sautin dariyar Engr.Dangi ce ta sanya Dr.Karami kara gasgata maganarsa. "seriuos Wallahi Safeenat tayi maka kani yana nan mai kama da kai". "Masha Allah nayi farin ciki gaskiya Allah ya raya ya dayyaba amma gaskiya Baby din nan bai iya zuwa ba sam sai da ya bari na baro garin sannan zai duro duniya mai makon tun dadynsa na can ya kamata ace ya zo". Engr.Dangi yasa ke kecewa da dariya kafin ya ce, "kai Dalla waye dadyn nasa kai kasan a matsayin kani yake a wajan ka ni ne dady wallahi domin ba wanda zai kalli tazuru irin ka yace masa Dady don haka becarefull". In da sabo ya kamata ace Dr.Karami ya saba da tsiyar da abokin nasa yake yi masa na rashin aure domin in sau goma.za su hadu sai yayi masa gorin mata amma sam haka bai ɗaɗashi da kasa ya san komai nufin Allah shi kasan yana son yin auren But bai san dalilin da har yau bai ga matar da ta kwanta masa har yake tunanin zai iya zaman aure da ita ba yanzu in bai manta ba yana 32years kenan a girma ya girmi Engr. Dangi da kusan shekaru Uku amma gashi nan har ya riga shi aure har matar tasa ta haihu. Gyaɗa kai kawai yayi ya shiga cikin falon bayan ya bude dakin sa ya dosa yana shiga ya ajje wayarsa da key dinda ya zare suit din dake jikin sa ya ajje sannan ya cire fara rigar mai dogon hannu ta cikin suit din ita ma ya ajje sannan ya cire dogon wando bayan ya cire takalmin kafarsa ya tsaya daga shi sai Boxer da singlet Toilet ya nufa ya watso ruwa bayan ya fito ya tsan jikinsa sosai da sosai jallabiya ya zurawa jikinsa mai ruwan jinin kare wanda tayi matukar dacewa da jikinsa sosai Coffee yaje ya samarwa kansa mai zafi sosai sannan ya dawo cikin dakin sa ya zauna kan daya daga kujerun dake dakin sosai da sosai ya nutsu yana shan Coffee din a hankali duniyar tunani ya je fa kansa wasu abubuwa da ya ajje can kasar zuciyarsa ya ji su yo masa sama yana sake maimaita su sosai ya shiga tunano Dr.Aqeel da abin da ya wakana a cikin asibitin sosai yake tuno yar matashiyar budurwar nan da ya jima yana nazarinta wanda ashekaru ba zata haura 15years gyaɗa kai kawai yayi gami da murmusawa. [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA GOMA SHA DAYA. Sosai yake kaiwa da komowa cikin dakinsa, hannayensa sarke a kirjinsa, lokaci-lokaci ya kan ja tsaki kamar harshensa zai tsine. duk sanyin da A-C din dake dakin take bayarwa hakan bai hana gumi samon mazauni saman goshin sa ba. Sosai ya cigaba da zarya a dakin cikin rashin mafita akan abin da ya addabi zuciyarsa sosai yake jin zafi da raɗaɗi a zuciyarsa da ruhinsa sosai ya ji komai da ya faru dashi kwanakin baya sun hanashi sukuni ya naji a ransa bai taba ganin 'ya mace da ta raina masa hankali ta ci masa mutunci kamar wannan kankanuwar ƴarinyar wanda ko a zaben mata aka saka ta ba in da zata kai labari kwaila ma irin ta wacce sam bata san Darajar da mace ke da ita a wannan duniyar rayuwar ba ta yanzu ba amma har ta dubi tsabar idon sa ta gaya masa haka. "Noo Impossible". Abinda ya fadi kenan cikin daga murya mai sauti yana faman kai wa kirjinsa naushi kamar a nan mai laifin take. Kamar wanda aka tsikara haka ya zari Key din Motarsa ya fara tafiya cikin sassarfa kamar zai tashi sama a haka har yafice daga cikin dakin sosai yake taka benen da zai kai shi zuwa kasa sashin babban falon cikin gidan kallo daya zaka yi fuskarsa ka fahimci halin da yake ciki na kunar rai sosai yake zakar wani abu a ransa wanda yake da tabbacin shi kadaine mafita gareshi dole ya dauki mataki dole ya dan hukuncin da zai dauka dole ya nuna mata tayi kadan ba kowan kowa bace a cikin jerin mata ba ta kai Level din da zata raina shi ba ba ta kai matakin 'ya mace da zai kalla har ya yaba ta raina masa hankali ba da wannan sakar zucci har ya fice daga sashin cikin gida ya doshi Mota Parkig ya fara kokarin fiddo da motarsa komai yake yin sa a hanzarce haka ya figi motar mai gadi na ganinsa ya doso shi da sauri ya mike ya nufi Get din ya bude sosai yake kallon fuskar Huzaif yanayin da ya ganta sai da gabanda ya fadi sosai. "Allah Yakyauta". Abin da ya fadi kenan yana margaya kai ya mai da Get ya rufe bayan Huzaif ya fice. Sosai yake gudu kan titi zuciyarsa na faman wassafo masa abubuwa ma bambanta sosai yake jin komai na zuwa masa a bazata wanda ya hakikance ba wanda ya assasa hakan sai wacce kwailar yarinƴar wacce ko kyautarta aka bashi ba abin da za tayi masa a rayuwarsa illah wahala. Cikin mintin nan da ba su haura talatin ba ya isa Kofar Asbitin baban alis sosai yake kallon asibitin bayan yayi parking ya fito yana mai wasa da Key din motartashi gaban motar ya usa ya yi tsalle ya hau gabanta ya zauna gami da harɗe hannayensa duk biyu a kirji ya kure kofar asibitin da kallo yana tunanin abin yi domin shi dai zuciyarsa ce ta kawo sa amma bai san takamaiman abin da zai gudanar ba abubuwa biyu suke masa sukuwa da tunanin sa haushin Mariya da kuma son ganinta wanda duk ya ajje a hurumi daya wanda sam ba su da alaƙa da juna numfasawa yayi gami da zaro wayarsa daga aljihu yana shuga dandannawa kamar mai kokarin kira kamar wanda ya ga takaici sai kuma ya ja tsaki gami da maida wayar aljihunsa yana faman sakin numfashi. ***** "na rasa me zan yi komai ya kwance mani". Abinda ta fadi kenan tana tura laɓɓanta cikin bakinta tana faman ya mutsa fuska kamar wacce aka sanya shan magani. Sosai yake kallonta da yanayin da take ciki na yanayin rashin kwanciyar hankali komai ya bayyana a fuskarsa na tsananin damuwa har zurmawa tayi kamar wacce ta tashi daga gudawa. "na rasa ta ina zan miki bayani ki fahimta, na rasa mai zance miki wanda zai ganar dake komai da komai kin kasa daukar abin da nake fada miki, ya zan yi dake Mariya?". gyaɗa kai kawai take yi tana faman dauke kwallar da taji suna kawo mata farmaki. "Hakuri Dr.Aqeel. bani da komai da zai taimaka min domin samun natsuwa ta ka tuna yau kwanansa Biyar ban gan sa ba, yau kwanan sa biyar ban san a wani hali yake ba, dole dole ne na damu sosai da sosai zuciyata taki hakuri taki natsuwa". Ta karashe cikin karfin hali kamar mai som fashewa da kuka kai ta cigaba da gyaɗawa. "ban san abin da yasa yaki jin magana ta ba, ban san abin da yasa bai yi amfani da abin da nace ba komai da komai Dr.Karami yace zai amma yaki yarda da hakan". Ya fadi yana kallon Mariya wacce gabadaya hankalin ta na wajan Habeeba wacce take sharar barcin ta hankali kwance kamar bata da wata matsala a duniyarta mai da kai tayi wajan Mu'azzam wanda shi barci yake yi. sosai take jin tausayin sa na damunta a rai sosai take tausayawa rayuwarsa. Mikewa tayi ba tare da ta dubi Dr.Aqeel ba ta fara tafiya sannu hankali sai ka rantse rashin jini ne ke damunta. "Uhmm nace ba". Ya fadi yana mai kallonta cak! tsaya ba tare da ta juyo ba. "ina zaki kuma?". "waje zan fita". ta bashi amsa tare da kara saurin tafiyarta don ba ta so ta sake furta ko da kalma daya ne gareshi So take ta je waje ko za ta samu sa'ida a zuciyara ba wai ta yarda dari bisa dari bane a,a kawai dai zaman dakin ne ya fara gunduranta dalilin Dr.Aqeel ba ta son a daidai wannan lokacin ace maganar wani na ratsa mata kunnuwa tana bukatar natsuwa ko yaya ne amma ta lura Dr.Aqeel ba zai bata wannan damar ba sam! Ba ta san me yake nufi da ita ba ta rasa ina zata sa kanka ko yaya ne ta samu hutun rai da ruhi. "MACE ƘYANƘYAWA". Sautin muryaar da taji ne ya sanya ta katse tunanin da ta afka sosai gabanta taji ya bugu har sai da ta sanya hannu ta dafe tana ambaton 'innalillahi wa'inna ilaihir raji'un' Sosai ta fiddo da idanuwanta waje tana mai sauke so akan sa sosai taji komai yana kwance mata cikin kwakwalwarta. Gabadaya idanuwansu suka sarƙe sosai suke ƙallon junansu an rasa mai dauke kallonsa daga dan'uwansa fuskar Huzaif ba abin da take saki sai murmushi sabanin ta Mariya da take a cungune waje daya kamar wacce aka aikowa da mutuwar wani cikin dangi A hankali ya fara kokarin saukowa daga kan motar shi yana faman sakin murmushi wanda daka gan shi kasan akwai alamun tambaya akan sa. Sosai yake tunkaro ta gabanta na sake tsananta faduwa komai take ji na kanta na wargaje mata ba abin da zuciyarta keyi sai ɗaci sosai. Ba ta son ganinsa, bata muradin ganinsa cikin duniyar rayuwarta, ylta tsani shi a zuciyarta tun daga kalaman sa take jin wani irin ɗaci tun daga kasar ruhinta a dalilinsa sai dai wani bangare na zuciyarta sam yaki kin yarda da Huzaif domin kullum cikin tono mata sunan yake. "Yaa Allah!". Ta fadi tana mai haɗe laɓɓanta waje tana cusa su cikin bakinta a hankali take daura hakoranta akai tana dannawa kanta a kasa tana jin saukar numfashin Huzaif kusa da ita hakan yakara tsinka mata zuciya ji take kamar ta kurma ihu don haushi. "wai ke mai yasa kullum in za a ganki, sai an ganki tare da kunci ne?". Ya fadi yana kallonta sosai yana kallon yanayin Emotion dinta da ya sauya lokaci guda yana kallon yarda fuskarta ke wanzar da haushi da ƙi kuma ya tabbata akan sa ne Murmushi ya saki ganin tana kokarin barin wajan ya kai hannu ya riko mata nata hannu. Ai ji tayi kamar an daura mata garwashin wuta a hannun nata nan da nan jikinta ya dau wani irin Shock har sai da komai ya motsa a jikinta da sauri ta dago kanta sosai take kallon Huzaif da rinannun idanuwanta ji take kamar ta tsinke shi da mari don takaci da bakin ciki bakin tane ya fara motsi alamun son magana laɓɓanta dake cikin bakinta har wannan lokaci ta shiga motsa su. "Don Allah ka rabu dani!". Ta fadi cikin murya mai sauti da karamar tsawa a cikinta tana mai dauke kallonta daga gareshi bayan ta watsa masa wani mugun kallo. Sosai yake mamakin yar mitsilar yarinyar nan, da yarda take yin komai nata cikin rashin tsoro ko fargabar abin da zai je ya dawo ya lura akwai tsoro a zuciyarta sai dai bata barinsa yayi tasiri a zahirinta ba. A hankali ya saki hannunta da ya rike gami da jan guntun tsaki mara sauti amma hakan bai hana Mariya ji ba ko kallonsa ba tayi ba amma ta lura yaji haushin abin da tayi masa gyaɗa kai tayi ta fara hanzarin barin wajan amma maganarsa ce ta sanya ta saurin tsayawa. "mai yasa baki son mai sonki da alheri, na lura wani naki ne bashi da lafiya amma kin ki bani damar da zan samu ikon duba shi, ko da yake ban san abin da kike tunani akai na ba ni dai ban dauke ki na ajje a zuciyata ba akan wani mugun nufi sai dai na ajje ki a zuciya a dalilin tausayinki da jin kai". Sosai maganganunsa suka shiga shigarta ta ko ina sosai take jin sautinsu na haifar mata da wasu lamura a kasar zuciyarta sosai take jin tasirinsu a kasar ruhinta sosai zuciyarta ta fara kokarin gasgatawa tunaninta ya karbi lamarin a saukake sosai take ajje numfashi a duk wani kalma daya da ya furta a hankali ta fara kokarin kallonsa idanuwanta a dan tsuke bata bari tasirin maganganunsa sun fito zahiri ba ta fara motsa laɓɓanta. "bana tsammanin zan yarda waki bugun ya sake gintawa a tsakaninmu kasan ance dukan farko shine duka kuma ka lalata damar ka tun a karo na farko don haka ina mai rokan ka ka fice mani daga rayuwa bana so komai ya faru tsakanina da kai kaji ko kawai ka kama gabanka kowa yayi rayuwarsa ba abin da ya hada kifi da kaska balle kuma har su da zauna inuwa daya". yanayin yarda ta ajje furucinta cikin halin-ko-in-kula yayi matukar kara zafin zuciya gareshi sosai yake kallonta yana jin rashin wayon da ya nuna akanta har ya tsaya yar yarinyar nan na fada masa abin da ta so a ranta tsaki yaja sam bai lura ta wuce ba sai da ya fara motsa baki yana son yin magana sannan ya lura bata wajan naushi ya kai sa iska gami da cizon Laɓɓa sosai ya ke kallon kofar aasibitin domin ya hango shigarta sosai zuciyarsa take shiga kunci a hankali yana mamakin yarda akayi yake wahalar da kansa akan wannan halintar wanda ko a farkinsa ban yi zaton zai ganta har ta samu damar shiga rayuwarsa ba dole ya san abin yi dole ya dau mataki akanta domin tsana yake hangowa tasa a idanunta ya tabbata ta tsanshi haushi sa take ji a ranta har a bayyane a fuskarta. "l'm Huzaif!". Ya fadi yana nuna kansa da dan yatsansa yana mai sakin murmushi gami da gyaɗa kai ya juya ya koma motarsa da gudu ya fuzge ta ya bar harabar asibitin. ***** Sosai Dr.Karami yake aikinsa cikin kwanciyar hankali da kware a harkar cikin kwanaki talatin da biyar komai ya fara kamo hanyar samun waraka ga Habeeba ba wai Mariya kadai ba hanta su Dr.Aqeel sunyi matukar yin farinciki da hakan domin sosai suke ganin komai na zama Normal izuwa wannan lokaci Habeeba ta fara samu sauki sosai don yanzu duk na fizge fizge da rashin magana ya kau sai da lokaci-lokaci in kana hira da ita tana kau ce hanya cikin hirar zaka ji tana wani zance na daban wanda bashi kuke yi ba hakan ya so damunsu Mariya sai dai Dr.Karami yana kwantar musu da hankali gami da sanar da su dole hakan sai ta faru gareta a hankali komai zai daidaita kamar bata tabayin cutar ba. Kamar ko yaushe yau mariya ce zaune ita da Dr.Karami suna hira domin shakuwa ce ta shiga tsakaninsu sosai da sosai Mariya tana matukar girmamashi gami da kunyarsa hakan yasanya Dr.Karami yake jinta a ransa sosai take burgeshi komai nata yanayi masa musamman da ya lura tana da hankali gami da natsuwa sosi a rayuwarta gata da gamun kai. Dr.Karami ya numfasa bayan ya gama wayar da yake yi ya dubi Mariya da take ta faman wasa da Mu'azzam dake hannunta shikuma yana faman ƙyalkyala dariya. Murmushi yayi yana gyaɗa kai kafin ya motsa laɓɓansa. "Na lura sosai da sosai ki ke son Mu'azzam, anya za ki iya rabu dashi kuwa in wani abu ya taso na zuwa wani waje". Kasa tayi da kai alamun jin kunya sosai ya kureta da ido. "kin fiye kunya Mariya anya kuwa". ya sake fadi yana dariya. A hankali ta dago kanta ta kalle shi sannan ta ajje kallonta gefe. "Uhmm Dan'uwana sosai nake son sa ban son rabu dashi ko na sakanne". "kenan yanzu ko lokacin aurenki yayi ba zaki iya rabu dashi ba a matsayin ki na 'ya mace yar gidan wani". Ji tayi kamar ta tsune kasa don kunya dalilin aure da ya ambata gabadaya sai ta rikece sai motsu motsu take yi ta rasa abin yi gabadaya. "wai shin ina zancen makarantarki ya kwana ya kamata ace kin koma makaranta Mariya zaman haka ba zai haifar miki da ɗa mai ido ba ke 'ya mace ce sosai karatu ke da muhimmanci a rayuwarki ya kamata ace kin mai da hankali sosai zuwa ga karatun ki ita ce dama daya jal da kike da ita ko don taimakawa iyayenki wata rana kece babba ko da dai ke yar gidan wani ne amma duk da hakan kiyi karatu". Sosai kalamansa suke samun masauki a zuciyarta sosai take jin dadin yanayin furucinsa cikin sanyin murya mai cike da karfafawa zata so ace hakan ta kasance gareta zata so ace ta samu wannan damar za ta so ace tayi karatu na sosai da sosai domin ta lura karatu a rayuwar zamanin nan yana da muhimmanci sosai musamman 'ya mace ko ba don komai wasu abubuwan na rayuwa da suke gudana a duniyar nan ya kamata ace mata suna samun wannan damar domin wasu fannonin 'YA'YA MATA ya kamata ace a wajan ba maza ba musamman harkar likitanci ko ba komai taimako ne na al'umma ku hakan zai wuce takaicin da wasu ke yi wa mara hali a rayuwarsu. Sosai take jin tausayin kanta da na iyayenta da kaninta Mu'azzam ta sani ƙaddara ta fado rayuwarsu gami da talauci da ya hana su gudanar da wasu abubuwa sosai da ya kamata ace sunayin sa ba wai rayuwar jindadin duniya take nufi ba a,a wasu abubuwan a rayuwar dangin rai dole yayi a karan kansa ba wai sai ya tsaya wani yayi masa ba musamman duniyar zamanin nan a yanzu in baka dashi ba mai yi da kai balle ya ya jikanka ta sani a duniyar nan in baka dashi kai da banza duk daya ne ta gani an aikaice akan ta anyi mata. Hawayen da suka zubo mata ne ta sanya hannu ta dauke su sosai take gyaɗa kai ta na son yin magana amma ji tayi wani abu mai nauyi ya saukar mata a kirhi sosai take jin komai na rashin dadi na wanzuwa a gareta sosai take tuno rayuwar da tayi a makaranta da irin yarda ake korota dalilin rashin kuɗi sosai take tuno yarda ake mata gori a makaranta kowa ya gujeta ba ta da kawa ko daya domin ta fita zakka a cikin yaran makaranta kullum cikin rashin babu take ba ta ga watan da zai ya kare ba a ƙore ta ba ta ranar da zata zo har ta fadi ba a tuhume ta da rashin babu ba akan wani abun bukata a makaranta. Kasa tayi da kai sosai take jin kuncin rayuwar da take yi sosai take hango ƙaddarar da take da wainiya da rayuwarta ita da ahalinta. "Mariya!". Sautin muryar Dr.Karami ta sauka cikin kunnuwanta wanda gabadaya ta mance ma da wanzuwan sa a wajan a dan razane ta dago da koɗaɗɗun idanuwanta ta sauke akan sa. "karki ce da ni ba ki son karatu, karki ce dani maganar da nayi miki ne ta sanya ki kuka". Kai ta shiga girgizawa sosai hawaye da sauka a kuncinta a hankali tashiga motsa laɓɓanta. "ko daya ba ruwanka komai naka gaskiya ne mai kyau ne sai dai...". Shiru tayi gami da yin kasa da kai sosai ya kafe da ido don ya gama fahimtar inda ta dosa da batun nata amma nauyi ya hanata fadi tausayinta sosai yake ji komai nata na rayuwa yake tausayawa. "Karki damu Mariya nayi miki Alkawari...". "Dr.Karami". Sautin Muryar Dr.Aqeel ne ta katse masa maganarsa tsaye yake ya harɗe hannu a kirjisa fuskarsa kadaran kadahan gabadaya ke kallonsu sosai yake son fahimtar abin da zuciyarsa take sanar dashi sosai yake kallon yarda Mariya take kuka wanda sam bai da sauti sai na hawaye sosai ya fara jin wani iri a kasar ruhinsa da zuciya zargin Dr.Karami yake da shiga rayuwar Mariya ya kunsa mata wani abun wanda yasanya shiga damuwa sosai. "na lura cikin yan kwanakin nan wani lamari ne yake tsakaninka da Mariya, in dai har za ku zauna tare bana taba ganinta ta tashi da dadin rai". gabadayan su suka dubi Dr.Aqeel wanda shi kansa sai da ya tsargu sosai akan maganar da yayi duk sai yayi wani zuru zuru dashi yana faman yake. Dr.Karami yayi murmushi domin ya rasa ina zai ajje zancen Dr.Aqeel bai fahimci in da ya saka gaba ba gabadaya tunaninsa ya tsaya akan zarginsa yake yi kenan da kuntata rayuwar Mariya? girgiza kai yayi kafin ya fara duban Mariya sannan ya dubi Dr.Aqeel. "ce maka tayi ina takura mata hala?". Sosai Dr.Aqeel yake nuna nadamarsa akan abin da yace ya san tabbas maganar da yayi ba ta da hurumin da za a ajjeta sosai ya shiga girgiza kai yana faman ajje yake kamar wanda aka baiea kyautar bazawara. "Noo ba haka nake nufi ba". Sosai su duka biyun suka kureshi da ita musamman Dr.Karami da ya fara hasaso wani abu da zuciyarsa ke sanar dashi amma yaki yarda da hakan mikewa yayi a hankali yana mai duban Mariya. "ni zan tafi sai gobe kuma ki kula da kan ki sosai". Gyaɗa kai kawai tayi alamun amsawa sai dai har ga Allah bata so tafiyarsa ba har a ranta tana jin dadin zama dashi amma ta lura Dr.Aqeel yana yi mata kanzagi akan hakan kamar ba ya so zaman da suke yi a tare tashi tayi tana duban Dr.Karami da yake yiwa Dr.Aqeel Sallama. "Nagode sosai gobe Allah ya kiyaye hanya ya tsare". ta na gama fadin haka ta gyarawa Mu'azzam kwanciya a kafadatar ta yi hanyar dakin da Ummanta take tana faman saka da warwara akan Dr.Aqeel gabadaya ta lura dashi ya fiye takura sosai duk da dai shi mai ALHERI ne amma wani lokacin abin da yake yi sam bai dace ba ya kamata ya san wani abu guda ba kowa ne zai iya daukar irin halin da yake nuna wa wanda zai san shi ba sai yaga kamar tsana ce kawai ko da ita a karan kanta ta fara dasa ayar tambaya akansa mafiya yawan lokaci in dai suna tare da Dr.Karami yana yi mata wasu abubuwa kamar natsana ita da Dr.Karami din ta rasa in ya dosa ta rasa menene nufin sa da hakan din. Tsaki ta ja kamar harshenta zai tsinke ta karasa shiga dakin kwance ta sameta tana barci samun waje tayi ta zauna izuwa lokacin Mu'azzamn barci ya fara tafiya dashi sosai tashi tayi ta shimfiɗar dashi ta sannan ta samu gu ta zauna ta zabga tagumi ta fada duniyar tunanin mahaifinta wamda ba ta san a wani hali yake ba cikin duniyar rayuwarsa tun fitarsa kwanakin baya da yayi har yau ba alamun sa ta rasa ina ya tafi ta rasa mai yasa mahaifinta yayi mata haka ta ba so yayi misa da ita a kowani hali suka tsinci kansu tasani rashin abubuwa yana taka muhimmiyar rawa a duniyar rayuwarsu sai dai ba yarda za suyi ta sani rashin babu ne yasanya mahaifinta fita amma bai dace ace tsayin wannan kwanakin ba asan a inda yake ba har gida taje amma ta sami labarinsa ba sai ma rashin mutunci da Goggo Marka ta aikata mata da kuka ta baro gidan. Sosai take jin faduwar gaba game da mahaifinta duk lokacin da take tunanin sa komai take ji bai mata dadi a rai ta rasa mai za tayi ta rasa mai ya dace tayi sosai kwakwalwarta ke caji wanda ita kanta ta san tunanin da take sanyawa kanta ya fi karfin kanta sai dai bata san mai za tayi ba komai a cakuɗe yake cikin duniyar rayuwarta. [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA GOMA SHA BIYU. Sosai idanuwansa suka kaɗa sukayi jajir kamar wanda aka watsawa garwashin wuta. Sosai yake jin wani zafi da zugi a kasar zuciyarsa sosai da sosai kirjinsa yana wani irin bugawa kamar zai rabe gida biyu numfashi yake ajje wa lokaci-lokaci mai tsananin zafi da zugi. Shisha din dake girke a tsakanin kafafuwansa ya zubawa ido sosai kamar wanda yake son fahimtar wani abu game da ita a hankali ya kamo yar igiyar da ake amfani da ita ya kai bakinsa ya zuga tsayin sakanni talatin kafin ya zare daga bakinsa gami da sakin wani hayaki wanda ya turke masa fuska gabadaya ya kasance ba ka hango kansa ma sosai hayakin yake tuntulowa daga bakinsa da hancinsa sai da hayakin ya debi lokaci kafin ya tsagaita da tuntulowa sosai idanuwansa suka kaɗa har da yar guntuwar kwalla kwance a ciki. Gyaɗa kai yake faman yi ba abin da yake yi masa shawagi a duniyar tunaninsa da zuciyarsa sai wani lamari da ya kasa gasgata shi ya rasa a ina zai ajje shi domin samun saukin raɗaɗin zuciya dana ruhi sosai yake jin nauyi a kirjinsa sosai komai ke kwance masa na tunani sosai yake jin abubuwan da suke addabarsa suna amsa kuwwa gami da sauti a kunnuwansa kirjinsa yake ji yana kara nauyi sosai numfashi ma dakyar yake samun ajjeshi. A hankali ys ajje igiyar shisha din ya fara yinkurin mikewa wani irin nauyin kirji ya sake tokareshi daga hanzarin da ya so amfani dashi da sauri ya koma ya zauna ya na mai sakin numfashi da sauri-sauri kamar wanda aka sanyawa Oxgyen sosai yake jin bacin rai in ya tuna kalma guda da yanayin da take furtata akansa sosai yake jin ɗaci a ruhinsa akan duk kan wata kalma da ta fito daga bakinta sosai yake jin zafin tsakin da tayi masa a daidai wannan lokaci. Mai yasa... Mai yasa mai dauki mataki tun a waccan lokacin ba, mai yasa ya bari damar ta subuce masa mai yasa yake kasa aiwatar da duk wani kudiri da ya daukarwa kansa in har yana kusa da ita ya rasa dalili. Zancen da yake ta saƙawa kenan a kasar zuciyarsa sosai yake ganin tana yi masa kwarjini a idanuwa sosai yake kasa aiwatar da komai in yana gabanta. Kai ya shiga girgizawa yana faman taunar laɓɓansa kamar su ne masu laifin sosai yake jin komai ya cushe masa sosai yake ganin kwanciyar hankalinsa na guje masa sosai komai ke shirin ƙwaɓe masa a rayuwa a dalilinta a matsayinta na kaskantaciya wacce bai dauka a bakin komai ba. "Ni Huzaif ni ta wulakanta". da sauri yake girgiza kai ya nasake furta. "ya zama dole nasan abin yi zuciyata ba zata yafe mani ba sam! na lura da hakan". Haka yake ta sakin zance kamar wani zararre tsayin lokaci kafin ya mike cikin karfi hali ya fada Toilet ruwa ya watsa wa kansa nan ya fito ya shirya domin ya lura in har yana zaune a waje daya komai zai iya hanashi sakat! musamman kan maganar yarinyar da yake ji a ransa ya tsana tsana mai tsanani. ***** "Please Khairiyya!". Ya fadi cikin wani irin yanayi mai wuyar fassaruwa a gareshi sosai yake jin zafi a zuciyarsa sosai yake jin ko ina na zuciyarsa na yayyagewa sosai kansa ke sara masa komai ya kwance masa sosai ya shiga tashin hankali mara yankewa wanda yake tsammanin zai iya tafiya da numfashin sa. Sai da ya gama ja-in-ja da numfashin sa kafin ya daga laɓɓansa daƙyar. "Ina cikin Matsala sosai da sosai na rasa ya zan yi komai yake kwance mani na tunani na komai zai iya faru ki taimaka ki zo". A wannan karon muryarsa ta rage sauti sannan kuma tana rawa hannayensa duk biyun ya daura akan sa bayan ya sauke wyar daga kunnansa sosai yake jin tashin hankalin da ya tunkaro shi sosai yake jin bugun zuciyarsa na sauyawa daga kwanciya hankali zuwa akasinsa. "ban san abin da ya sanya ni gamu da ita cikin duniyata ba, ban san abin da yasa ta shigo rayuwata ba ban san abin da yasa ranar ta zo mani a haka ba ban san mai yasa tsautsayin da nake gudu yake kokarin fado mani ba ban san gangancin da ya kai ni wannan ranar har hakan take dauko mani tashin hankali wanda ba zan iya dauka ba". Gabadaya ya zube kan cafet din dake tsakar dakin yana faman sakin numfashi a hankali ji yake yi kamar gabadaya tashin hankalin duniya a kansa ya kare. Marikin kofar da yaji an murza ne ya sanya shi saurin buɗe idanuwansa da suke rintse sosai yake kallonta da yanayin da ta shigo dashi kau da kai yayi gami da jan gudun tsaki wani haushi ne yaji ya tokare masa wuya ji yake kamar ya tashi ya rufe ta da duka sai yanzu yake dana sanin kiranta bai san dalilin da yasanya shi kiranta ba wani haushi yake ji a game da ita gabadaya yake ganin muninta da wani haushi nata yana tun karoshi mai da idanunsa yayi ya rufe. Ita kuwa ganin irin Halin-ko-in-kula da ya nuna mata sai ta dauke kai tana mai jan tsaki a hankali ta fara taku har ta isa kan daya daga kujerun falon ta zauna kafin ta dube shi sosai kallo take masa na TUHUMA sosai take ganin sauyi gareshi sosai take ganin komai nashi ya sauya ba yarda ta san shi ba kyaɓe baki tayi kafin ta motsa laɓɓanta da suka sha Pink din jambaki. "Huzaif". Ta fadi a hankali tana kara kureshi da idanuwanta manya masu kalar madara sai faman kaɗa su take yi. Bai motsa ba balle ta saka ran masawar sa sosai taji haushin haka amma bata nuna ma sai ma sake kiransa da tayi nan ma bai amsa mata ba hakan ya kara kular da ita a zafafe ta mike ta fara kokarin barin falon tana fadin. "A rayuwa na kijin wulakanci zan iy daukar komai amma ban da wulakantawa kuma wannan zai zama karo na karshe wallahi!". tana gama fadin haka ta rike murfin kofa tana kokarin murɗawa ta fice. Huzaif da yake fama da zafin zuciya ya kokarta buɗe idanuwansa ya sauke akanta. "Khairiyya". ya fadi a raunane ita kanta sai da taji wani iri a jikinta a sanyaye ta saki kofar gami da juyowa ta dube shi tana harɗe hannayenta a kirji. "Taimako nake bukata don Allah". Da mamaki take dubansa tana juya maganar tasa akanta kafin ta yi taku uku sannan ta tsaya. "Huzaif taimako fa kace?". Kai ta shiga girgizawa tana faman sakin yaƙe. "me ke damunka har kake neman taimako a duniyar nan?". Ta sake fadi tana mai kafeshi da idanu sosai. "Nima ban sani ba komai ya kwance mani kawai ji nake kamar bani ba...". Da hanzari ta tare shi. "Ban gane ba Huzaif?". Tashi yayi daga kwancen da yake a hankali ya mike tsaya sosai yake kallon Khairiyya sosai yake hango zata iya taimaka masa sosi yake ganin ita kadaice zata iya yi masa komai da yake bukata. Gyaɗa kai yayi kafin ya ciji laɓɓansa hannunta ya kamata ya fara kokarin ja da sauri ta fizge tana masa kallo mai dauke da TUHUMA shima kallonta yayi wani iri kafin ya sake jan hannun nata suka fice daga cikin falon. ****** Sosai ya zuba musu ido yana jin wani iri a gameda su gabadaya zuciyarsa ta ki yarda da su sosai gabansa yake faduwa ji yake kamar akwai mugun nufi a tattare da su sosai ruhinsa da zuciyaesa suke nuna masa shakka akansu idanuwansa sosai yake dubansu da su tun da yayi Parking a harabar asibitin ya tokare a jikin motarsa kira BMW yanayin su kawai yake kallo yake hango rashin gaskiya da kuma tashin hankali a tattare da su a hankali ya fara takunsa cikin natsuwa idanuwansa na kan su har izuwa lokacin kofar da zata sada shi da cikin asibitin ya dosa sai da ya zo daidai da su gabadayansu idanuwansu suka sarƙewa juna wani irin kallo suke duban junansu dashi kamar wanda suka san juna da jimawa zuciyoyinsu sai fama kawo musu wani lamura suke ma bambanta wanda su akaran kan su ba su na me nene ba. Kau da kai Dr.Karami yayi da sauri yana gyara zaman niktayal din wuyarsa ya cigaba da takunsa ba tare da ya sake bi ta kan su ba har ya isa cikin asibitin. Sannu a hankali ya fara takunsa yana ajje wa dakin su Mariya yanu fa yana kokarin sa kai itama ta sanyo kai zata yo waje kamar daga taji a kirjinsa da sauri cikin yanayi na firgici ta ja da baya tana mai zare idanu. "Subhanallah!". Ta fadi cikin tsanani kaɗuwa sosai take kallonsa shima idanuwansa na kanta sosai yaji wani irin Shock a ko ina na hanyar jininsa har sai da ya runtse idanuwansa domin ji yayi gabadaya kansa ya shiga juyawa kamar wanda wayar wuta ta zukar wa jini yayi low sosai "Don Allah...". Ta fadi tana mai rawar baki idanuwanta ta sauke su kasa sosai da sosai take jin ko ina na jikinta na sauri jininta yana kara gudu zuciyarta na kara sauti wajan bugawa. Hannu ya daga mata yana mai sakar mata murmushi gami da lumshe idanuwansa sosai yake fuskartar natsuwar da take dashi sosai yake jin tana burgeshi duk da kananun shekarunta amma hankalinta na yanayin natsuwarta kamar mai shekaru sama da ashirin ko da yake duk wanda ya ganta ba zai taba bata haura shekaru sha biyar domin Mariya tana da tsayi da kuma kaurin jiki irin matan nan ne masu diri da cikar matantaka sosai ta ko wani fanni sosai jikinta yake bayyana irin baiwar kirar jikin da Allah ya bata ko ina na jikinta sosai ya cika sai dai ace yarinya ne a jikinta rintse idanuwansa yayi jin zuciyarsa na hasaso masa abubuwa ma bambanta da sauri ya zare tunani ya ajje gefe yana mai sauke numfashi. "Yaa Allah! Mariya zaki fasa min kirji ko". Ya fadi yana mai haɗe girarsa kamar gaske yanayin da ta dan razana ta dago kamt da sauri tana kallonsa lokaci guda idanuwanta sukayi rau-rau kamar za su zuvda hawaye. "Don Allah...". Da sauri ya kai dan yatsarsa bakinsa gami da furta. "Shiit". Yanayin yarda yayi salon sai ta saki baki tana kallonsa sosai taji ya burgeta da yanayin da murmushi ya sauka a fuskarsa ta tabbata wasa yake yi mata kasa tayi da kai ta dag laɓɓanta. "Ban sani ba, ban san kana taho wa ba na rokeka...". "Nace kiyi shiru mana!". Ya fadi muryarsa da dan sauti a cikinta. Gyaɗa kai ta shiga yi tana kokarin giftashi ta wuce ya tae ta da cewa. "Ina kike kokarin zuwa?". Shiru tayi tama rasa mai za tae dashi sai juya faka din dake hannunta take mai dauke shara. Sosai ya gane in da ta dosa amma so yake yi tayi magana da kanta amma ya lura magana ma wuya take mata "koma ciki to tunda ba in da zaki". Da sauri ta dago kanta tana kallonsa yanayin da taga ya ci mur ta san da gaske yake baki ta fara motsawa. "Shara...". Abin da ta fadi kenan ta tsuke bakinta ta sake yin kasa da kai tana cigaba da wasa da fakar dake hannunta gabadaya taji gajiya na saukar mata sosai ta matsu ta bar wajan amma ta lura Dr.Karami sai ya ga kafarta ta zubda ita kasa sannan zai rabu da ita. "Ya jikin Umma?". "Da sauki". Abin da ta fadi kenan domin ta lura in dai yayi magana bata amsa ba hakan ne zai sanya ya hanata tafiya. "Madallah! zaki iya tafiya". Kamar wacce take jira da sauri ta fara jan jikinta har tana kokarin tuntuɓe sosai yake kallonta yana kallon yarda take ajje taukunta duk da dai cikin yanayin tsoro take amma hakan bai hana bayyanar da natsuwa a takunta ba sai da ya ga fitarta sannan ya numfasa ya karasa shiga dakin. Tunda Mariya ta fice take gayyato natsuwa tana yafawa kanta sodai tsoro da kunyar Dr.Karami suke samun mazauni a zuciyarta sosai komai nashi yake burgeta sosai take jin wani iri in suna tare sosai zuciyarta ke natsuwa in suna tare amma a zahirince tsoro ne ke bayyyana a fuskarta ta rasa dalili ko da yake zata iya ajje hakan a matsayin Kwarjini da yake mata sosai musamman yanayinsa da cikar halintar mazanataka da yake dashi sosai take jin wani iri in tana gabansa sai ta raina kanta sai taga kamar dan tsako ne a gaban rakumi. Har tasa inda za ta zubda sharar bata daina zancen zuci ba saura kadan ta afka cikin dan wajan da aka tanada don zubda shara ita kanta sai da taji kunya da sauri ta zubda sharar ta juyo domin komawa cikin asibitin taku kadan tayi da yake kanta a kasa yake sam ba ta lura da wanda yake gabanta ba gabadaya ta ji ta ci karo da mutum sosai ta tsoro zuciyarta lokaci guda ba wanda ta kawo mata sai Dr.Karami tunanin ya kawo mata wato yana biye da ita kenan lokaci guda ta sake tsora a ranta tana fatan Allah yasa bai ga halin da take ciki ba a dalilinsa. Tunaninta ya tsaya lokacin da taji wani wari gami da kamshin tuarare sun haɗe waje daya sun ba da wani kamshi mara dadi don sai da taji zuciyarta ta fara tashi da sauri cikin tsananin haushi da takaici ta dago kanta ta sauke kan mutumin da ya kusan tafiya da numfshinta da sauri ta ja baya tana mai zare ido bakinta na ƙarkarwa sosai take kallonsa gabadaya take jin tsoro da dukan zuciyarta na karu yanayin da ta ga idanuwansa sun kaɗa sunyi jajir har wani launi duke sauyawa nan da nan ta shiga waige waige domin neman hanyar cetar kai sai dai sam hankalin mutane da suke kai kawo baya kan su da sauri ta ja da baya tana ambatar sunan Allah a zuciyarta lokaci guda ta ji wani irin takaici da haushinda ya sake turnuke ta kau da kai tayi domin ta fusakanci rainin hankali tsantsa yake son kawo mata sabo ya rainata ya raina girmanta ya ganta kankanuwa shiyasa ya sami lasisin da zai shigo rayuwarta ya yi abin da yake so saboda ya mai da ita marashin 'yanci in ba wai tanuna masa zahirin ta bane ta nuna masa ita ma mutum ce kuma ta san darajar kanta ba za su zauka lafiya. "Na rokeka da Allah da Annabi ka fice daga rayuwata amma ka ki ji ko to bari in hadaka da Iyayenka kila a dalilin su ka bar ni". Ta fadi tana kara tsuke fuska sosai idanuwana kansa amma sam bata ga yanuna wani alamun yin wani abuba sai ma kara wani yaƙe yake yi saman fuskarsa haka kular da ita sosai. "ban san mai nayi maka ba, ban san mai yasa kake kokarin shigowa rayuwata ba, ban dan abin da ka gani a duniyata ba har kake kokarin shigowa na rokeka ka fita harkar ta bana bara ma da kai ko miskala zarratin". "Mariya!". Sautin muryarsa da ta doki kunnuwanta sosai hakan ya kara tsinka mata zuciya amma hakan bai sanya tsoro ya bayyana a fuskarta ba. "karka sake kiran sunana kuma ina mai rokon ka da karka sake batar sunana mai so ka ajje sunan Mariya a matsayin wanda baka taba sani ba ko a Mafark...". Gabadaya taji hannunta cikin nasa ya sarƙe waje daya ba ta san lokacin da ta saki fakar dake hannunta ba cikin tashin hankali tana kokarin kware baki ta kurma ihu taji ya saka dayan hannunsa ya rufe mata baki nan ta kara hargitse tana faman zille-zille domin kwatar kai amma ina ta kasa domin ji take kamar wacce aka daure da sarƙa idanuwanta suka kara yo waje sai faman nishi take yi amma ko a jikinsa sai ma faman murmushi da yake yi idanuwansa na kara hargitsewa waje guda a hankali ya zare hannunsa daga bakinta hakan ya ta damar sakin ihu amma ba mai sauti ba ganin irin alamu da yayi mata alamun shiru. "kin fiye tsiwa Mariya". Ya fadi yana kara sarke hannayensu waje daya yana murzawa kadan sosai take jik wani iri a jikinta ko wani sashi na hanyar jininta take jin yana tsayawa cak! da aiki sosai sumar wucin gadi ta ziyarceta a hankali ta fara rintse idanuwanta tana jin tashin hankali na samun ma sauki a kowa ni sashi na jikinta zuciyarta na kin abin da yake mata tsanarsa take ji sosai da sosai tana jin haushinsa na samun matsuguni a zuciyarta. Sosai wani sashin zuciyarra ta shiga biya mata karatu. 'Ke fa mace ce akan mi zaki tsaya wani namiji gardi yana rike miki hannun kin san illar haka kuwa shin ko kin manta kalamansa da yake fadi miki a haduwarku ta farko'. Sosai zancen zucin ta yayi tasiri a ko ina na sashin jikinta abin zuciyarta take sanar da ita a yanzu shi kawai ke amsa kuwwa a kunnuwant sosai take jin tana da karfin gwuiwar aikatawa in dai ita kadai ce hanyar da zata kwai kanta da mutuncinta. Tun da Mariya ta kulle idanuwanta ya zuba mata idanu sosai yake kallonta sosai yake kallon fuskarta da laɓɓanta da suka tsuke waje daya sun yi jajir da su hancinta dan madaidaici mai tsayi idamuwanta da suke rufe haƙa suka kara bayyanar da girmansu yake sosai yake jin zuciyarsa na sauya salon wasu lamurka sosai yake jin komai na kwance masa sosai yake kallonta tana burgeshi. Mariya da ta buɗe idanuwanta a daidai lokacin shi kuma ya shigar da laɓɓansa cikin bakinsa yana lasa ba ta san lokacin da ta daga hannu ta sauke masa zara-zaran yatsunta a kan kuncinsa ba ji kake Tasss!!. "ji ba yar iskan ba ce ka sani ni 'yar mutunci ce kuma iyayena masu mutunce ne sun san daraja da kimata ba wai sun haifeni bane don kowa ni dan duniya ya zo wajena ya yashe ka sani ni da kake gani nafi karfin ka wallahi bar ganina karama wanda yake baka lasisin zuwa gareni da mugun nufinka to ka sani nayi maka nisa wallahi na wuce da saninka ni ba irin 'ya'yan da ake ribata bane har a bata masu rayuwa don haka ka kiyaye". Ta karashe cikin yanayi na rashin tsoro ko abin da zai je ya dawo a da sauri ta fizge hannunta tana tsartar masa da yawu ta wuce abin ta. gabadaya komai nashi yaji ya tsaya na jikinsa sosai ya ji sa wata duniya wacce mai san ta mene ne ba sosai sosai yaji kansa na juyawa sosai yaji komai ya kwance masa gani yake yi kamar bashi ba gani yake yi wannan lamarin da ya faru kamar ba gaske ba gani yake yi ko a mafarkinsa ban yi tunani haka ta kasance ma dan yatsansa ya saka a baki sosai ya ciza shi kamar zai tsinkeshi zafin da yaji ya ziyarce shi ne ya sanyashi sauri buɗe idanunsa ganin lamarin gaske ne bai san lokacin da wasu kwala suka taru masa a idanu ba da sauri yayi kokarin mai da su yana mai dafe kirjinsa ba abin da yake hangowa sai hannun Mariya lokacin da ta daga ta sauke a fuskarsa ba abin da kunnuwansa ke jiyo masa sai yarda sautin marin ke sauka a kan fuskarsa. Sosai kalaman da ta furta suke dawo masa sosai yake jin wani irin yanayi na zarya cikim gudu suna samun masauki a ransa sosai yake jin wani katon abu mai nauyi na samun masaukin a zuciyarsa da kasan ruhinsasosai yake jin wani irin abu maɗaci da bauri na sarƙe masa harshe sosai kalmar MUTUNCIN tana dashi yake amsa masa kuwwa a ko wacce dakika gyaɗa kai ya shigayi gabadaya ya kasa motsawa lokaci mai tsayi ya dauka a haka har zuwa lokacin mai gama tantacce abin da ya faru dashi gskiya bane. "Uhm ai ita dama WUYA MAKARANTAR KARE ce wallahi". Abin da muryar Khairiyya ta fadi kena tana dosa in da yake sosai take masa wani irin kallo na raini da takaicin abin da ya faru sosai take jin ɗaci a ranta musamman yarda taga komai ya faru akan idom ta ba abin da y kara tsikar mata da zuciya sai Yainyar da ta gani wai akanta Huzaifa yake zaucewa ta rasa ma mai ya dace tayi ji take kamar ta tsinke shi da mari amma ina! ba za ta iya ba a hankali ta fara riko hannunsa ta na murzawa sannu a hankali ta fara jansa tamkar rakumi da aƙala har suka isa wajan motar gidan baya ta buɗe ta turashi cikin wani irin yanayi kamar wanda akayi wa dukan shan gishiri. Sai da ta kare masa kallo sosai da sosai tana kallon yarda ya rintse idanuwansa kirjinsa na harbawa da sauri-sauri kamar zuciya zata fasa ta fito kau da kai tayi jiki a sage ta koma gidan gaba wajan zaman direba ta shiga ta tada motar cikin wani irin yanayi ta fizgi motar har sai da kura ta tashi ta fice daga harabar Asibitin. [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA GOMA SHA HUDU. Hannu bibbuyu ta zabga tagumi idanuwanta kan Mu'azzam. sosai take kallonsa tana jin wani irin abu na sauka kan zuciyarta da ruhinta, sosai take jin wani abu mai kama da ruwa yana kwaranya a ko wani sashi da loko na ma'ajiyar zuciyarta, komai take ji yana yi mata wani iri sosai take jin kauna da so mai girma na saukar mata akan kaninta ba abin da take nisawa a ranta sai yarda duniya lokaci guda take shirin juye mata da wata irin ƙaddara mai girma a rayuwarta. sosai take jin duniyar na wargajewa da dukkan wani farinciki mai girma, da ta san tana samu cikin kankanuwar rayuwarta. Ya za tayi kenan in ta rasa wadannan madogaran rayuwarta ta mai duniyarta za ta kwaso mata in ta rasa wadannan mutane masu matukar muhimmanci a duniyarta. Wasu hawaye masu zafi matuka taji suna sauka akan fuskarta da can cikin zuciyarta da ruhinta. Ta sani kuma ta dade jimawa cikin duniyarta ba ta da sa'a a rayuwarta domin kuwa sosai ta fuskata ƙaddara mai kaifi ce ta fado mata da abubuwa masu matukar tashin hankali da yankewar farinciki Babanta ya tafi ya barta ga Ummanta bata da lafiya ga karamin kaninta wanda shi ƙaddara ta sunkuto shi cikin wannan duniyar mai dauke da kwamatsai rashin dadi ina ma tana da dama ina ma tana da iko ina ma ta san zai fado duniyar nan a haka da bata yarda ba da bata amince ba ina ma ace ana tuntuba kamin a sako dan'uwa duniya da ta roki ubangiji bai sako kaninta ba sai dai ba yarda ta iya komai na Allah tabbatacce ne a duniyar dangin rai kana naka yana nashi. Hannu ta sanya tana mai dauke zafafan hawaye da take jin su a ko ina na sashin zuciyarta tana dauke su wasu na biyo bayan su tana jima cikin wannan yanayin kafin ta motsa ganin Mu'azzam yayi barci ta kai shi makwancinsa ta kwantar bayan tayi Hugging din sa a ko ina na fuskarsa sosai take jin kauna mai girma a tsakanin ko ina na sassan jikinta akan shi sosai take hango wa a duniyar nan bata da kowa dangin yan uwa sai shi dole ta kula dashi dole ta so shi domin shi kadai ne take zaton zai shafe duk wani daci da kunci da ukuba da take ji a zuciyarta na rashin yan uwantaka. A hankali ta fara takawa har inda Umma take kwance ta na barci hankali kwance kallo daya zakayi mata ka tabbatar akwai alamun warakar natsuwa a tare da ita. Idanuwanta sosai ta buɗe akanta tana kallonta kamar wacce aka ce in ta dauke idanuwanta za a gudu da ita zuciyarta taji tana wani amsawa da wasu abubuwa mabambanta wanda ita kanta ba za ta ce me nene ba. Wani murmushi ya subuce mata kalaman Dr.Karami suke mata yawo a kunne a jiya bayan ya zo ya duba Umma. **** Kallonta yake yi sosai yana yawatawa da idanuwansa masu wani irin yanayi mai matukar kashe jikin wanda ake kallo sosai take jin kallon nasa na shiga duk wani sassa na jikinta yana haifar mata da wasu abubuwa wanda ba ta san a mizanin da za ta ajje su ba sosai take jin bugun zuciyarta sosai take jin yarda zuciyar ta ta take tsalle a duk wata dakika daya na kallon da Dr.Karami yake yi mata ta rasa mai yasa take jin haka ta rasa dalili lokaci da dama ana kallonta mutane masu muhimmanci a idanuwanta amma bata jin haka sai a kansa shi kadai kwallin kwal!. "Mariya". Yarda Dr.Karami ya ambaci sunan sai taji aduniyar rayuwarta bata taba jin wanda ya kira sunan da wani irin yanayi mai matukar amsa kuwwa a kwakwalwa da kashe jiki da sanya zuciya tsalle tsalle kamarsa ba sosai take jin duk wani sashi na jikinta na wani irin amsawa da narkewa kamar ana narka roba a wuta wani numfashi take ja mai matukar girma wanda take ji kamar in har batayi jarumtar jan sa ba numfashin katsewa zaiyi daga gareta kanta a kasa tana faman wasa da kasar rigar atamfar ta da take jikinta wanda kallo daya zaka yi mata kasan taji jiki sosai da sosai. "kin fiye kunya da yawa. Ya kamata zuwa wannan lokaci ki saki jikin ki da ni domin an zama daya". Wani irin kuwwa taji maganar tasa ta nayi cikin kwakwalwarta ji take kamar kasa ta tsage ta zurma ciki sam bata son yarda Dr.Karami ke mata amma kuma ta na son ta zauna dashi sosai a waje daya domin mutum ne mai saukin kai da kokarin kwantarwa da mutum hankali. A hankali take daga kai domin ita dai ba ta san mai zata ce dashi ba bama ta san yarda kalaman nasa su ke zuwa ba cikin kwakwalwarta ita dai kawai sautin muryarsa take jin na amsa amo nata. "kin ga dai yau kuna cikin kwana na Arba'in da takwas kin ga kenan yau saura kwana goma sha biyu su cike KWANA SITTIN da nace in Allah ya yarje mana komai zai daidaita a wajan Umma. Shin ya kike ganin jikin nata me kike karanta game da ita?". Ya dasa aya yana mai dubanta sosai cikin idanuwansa yana faman murmushi yana gyada kai sosai yake jin Mariya na samun masauki a zuciyarsa da duk kan wani sashi na jikinta sosai yake jin ta tamkar uwa daya uba daya suke sosai yake jin wani abu mai girma yana samun waje a filin zuciyarsa yana zama wanda a kullum yana jin yarda yake daɗuwa ba wai raguwa ba murmushi ya sake yi. "ban san mai zan ce miki ba, ban san ya kike rayuwarki bs, ban san mai yasa ba ki sakin jiki da mutum ba, ban san mai yasa kike gujewa mai...". Sosai yaji kalmar da zai fadi tayi nauyi a bakinsa ta danne harshensa da wani gingimeman abu mai girma sosai yake buɗe idanuwansa akanta wani irin bugu yake jin kirjinsa nayi bai san mai zuciyarsa take kokarin yi ba bai san abin da take kokarin dauko masa ba wanda sam bai yi tunanin haka ba. A hankali take dago kanta tana kokarin ajje idanuwanta akansa cikin yanayi na TUHUMA tana jin yarda zancen da yake yi ya yanke wanda take jin alamun akwai dalili kamar wani abu ne daban ya hana shi furta abin da yake kokarin cewa ko da dai ita akaran kanta ba ta san ina ya dosa ba kallo daya tayi masa ta kau da kanta jin yarda jikinta da zuciyarta sukayi wani irin tsalle. Girgiza kai ta shiga yi tana tura laɓɓanta cikin bakinta tana tsotsa kamar wacce ta samu alawa ta rasa mai zata ce masa bata san abin da ya dace ta ce dashi ba sosai take hango wasu abubuwa da suke rikirkita mata lissafin kwakwalwarta a idanuwansa sosai take jin abu mai girma game dashi sosai take hango kwarjini da haiba na dandatsa ko ina na cikin idanuwanta in ta dube shi can kasan makoshi ta fara kokarin furta wani abu a hankali laɓɓanta suka shiga motsawa. "Ban san yarda zan fuskance ka na ce da kai komai ba, ban san da harufan da zan yi amfani wajan cewa da kai komai ba amm...". Da sauri taja numfashi gami da tafiya da sauran abin da tayi niyyar cewa. Sosai ya ware idanu yana kallonta yana ganin yarda take datse laɓɓanta kamar wacce take tsoron furta wata kalma mai muni gareshi. "Fadi mana ko ya kike zo da maganar ki zan fahimta ba zan ajje ta a mizanin da bata dace ba". Ya fadi yana kara ware idanunsa sosai akanta wani matsayi yake jin ta na kara samu a gareshi sosai yake hango natsuwa da kula da kai tatttare da ita a hankali ya mike kan kafafuwansa yana duban in da Umma ke kwace tana barci Mu'azzam kusa da ita murmushi yayi kafin ya juyo ya dubi Mariya da take tsaye kikam! kamar wacce aka dasa gabadaya ta gama tafiya cikin wani irin yanayi, ba abin da take roko a ranta illa Dr.Karami ya tafi ko ta samu damar jan numfashi mai dauke da iskan Rahama. "na tafi Mariya tun da yau na lura azumin magana kike yi". Yana gama fadin haka ya fara taka kafafuwansa kamar da gaske tafiyar yake yi so yake yi ta dago ta kalle shi haka kuwa akayi tana jin tafiyar tasa tayi nisa gabadaya ta dago da idanuwanta aiko sai suka sarke da nashi ba ta san lokacin da ta saki kara ba gami da ja da baya tana runtse idanuwanta sosai ta sanya tafukan hannunta ta kara rufewa wata irin kunya take ji tana yawatawa a dukkan sasssan jikinta ji take kamar kasa ta tsage ta shige. Sosai ta bashi dariya ganin yarda tayi a hankali ya taka ya fice daga dakin yana faman sakin murmushi wanda shi kansa mamaki yake yi komai na Mariya na burge shi sosai da sosai. **** "Yaa Allah!". Abin da ta furta kenan tana sakin murmushi gami da dafe kai bata san abin da ya shiga kanta ba gabadaya take jinta wani iri sosai take jin ta a wani irin yanayi in tana zaune ko suna tare da Dr.Karami rintse idanuwanta tayi gami da jan numfashi wani kamshi ne taji numfashin nata ya jawo mata ya kai mata cikin hanci a dan firgice ta ware idanuwanta tana Ambaton Allah tsoron ta daya Allah yasa ba Dr.Karami bane domin ko tantama bata yi wannan kamshin nasa ne amma bisa mamaki ba kowa da ta gani ajiyar zuciya tayi tana dungurin kanta domin ta tabbata sharrin tunani ne kawai da na zuciya suke mata haka. ***** Dakiku masu dama ta dauka cikin motarta kafin ta fara kokarin buɗewa ta ziro kafafuwanta zuwa waje nan ma sai da ta ajje dakiku sannan ta fara kokarin ziro da gangar jikin zuwa waje ta mike kan kafafuwanta sosai take yawatawa da idanuwanta izuwa wajen da take tsaye tana faman yatsine fuska duk da bakin glass din da ya rufe mata idanu hakan bai hana bayyanar yarda take yi da fuskarta ba cikin wani irin yanayi ta tura murfin kofar gami da sanya mata secure kafun ta fara kokarin jan kafafuwanta. Sanye take da wasu kaya riga da wando fitted sosai wandon ya matse ta wanda iyakarsa gwaurinta mai kalar pink rigar dake jikin yar shara-shara ce mai kalar white da hannayen rigar ves ne wanda hakan ya bayyanar da rabin kirjinta sosai da ilahirin damatsan hannayenta fuskarta dauke take da Make-up sosai hakan ya kara ƙawata fuskarta ta laɓɓanta sun sha pink din jan baki sai daukar idanu suke gashin kanta ya ci gyara sosai sai fama daukar idanu yake yi ta barbaza shi a gadon bayanta a hankali take takawa saman takalamanta masu matukar tsine sosai komai nata motsawa yake a duk lokacin da tayi taku daya. Sannu a hankali har ta isa cikin wajan wanda kallo daya zakayi masa ka tabbatar da wani babban ma'aikace bene mai dauke da hawa goma sha biyu daga yanayinsa in ka kalla sai ka rantse ba a kasar najeriya yake ba. Kofar da zata sada ta cikin wajan ta dosa mutane da yawa masu harkokin gaban su sai bin ta suke da kallo na mamaki har ta isa kofar glass da take watayawa da mutane domin zuwa duk wani bene da suke bukata. Ba tayi kokarin barin baban Falon dake kasa na cikin ma'aikatar ba domin ba ta bukatar haka koma ta bukata dole tayi hakuri a dalilin rashin sanin in da ta dosa ko ta shiga yau ne karo na farko da ta tako kafafuwanta zuwa cikin wannan waje yau ne farko da ta fara ajje idanuwanta akan wannan waje a zahirance yau ne kuma take bukatar duk wasu mafarkanta su tabbata yau ne take so ace sun yi gaba da gaba da shi yau ne take so komai ya zo kamar yarda ta jima tana burin abubuwa daban-daban kafin wannan rana tana so ace wannan rana ta kasance cikin ranakun da nasarrorin ta za su fara shawagi cikin duniyarta yau ne take da yakinin lissafinta zai fara aiki kamar yarda ta tsara komai nata... "Madam!". abin da securty din wajan babbar kofar da suke zaune daya daga cikin su ya fadi kenan yana mai mikewa bisa kafafuwansa ya tsaya gabanta. Da sauri ta dawo daga duniyar tunanin da take yi ta sauke idanuwanta gabadaya akansa tana wani yatsine fuska gami da da sauke glass din fuskanta kadan manyan idanuwanta farare fes suka sauka akansa sai da ta gama kare masa kallo kafin ta gyaɗa kai cikin nuna halin-ko-in-kula gareshi. Shima bai damu da irin kallon da take masa ba haka ya sanya abin binciken dake hannunsa yana yawatawa dashi a sassan jikinta kafin ya dago kai ya dubeta yana mai bata hanya domin karasawa wani murmushi ta saki wanda ita kadai ta san in da ya saka gaba a hankali ta kama Handle din kofar ta tura cikin wani irin taku na musamman wanda kallo daya zakayi mata kasan akwai abin da ta taka karan takun takalmanta bisa tayal din dake shimfiɗe a harabar wajan duk ya karkato da mafiya yawancin mutanen da suke zazzaune suna gudanar da aiyukansu kowanne mutum daya akwai table a gabanda da kuma fiyal fiyal gefe guda kuma kwafuta ce girki tacin glass dinta take ƴawatawa da idanuwanta a dukkanin sassa da kowa ni mutum dake zaune sosai ta lura ita suka zuba wa idanu murmushi ta saki har gefen kumatun ta na loɓawa sosai taji wani abu na yawatawa a cikin kirjinta wanda take jin sa ba abin da ke cikin sa sai hango abubuwan da take tsammanin za su faru. "Heyy". Abin da ta fadi kenan gaban wani table da wata mace ke zaune hankalinta gabadaya ya ta'allaka ga aikin da take yi sanye take da jallabi mai kalar Ash ta nannaɗe fuskarta da kallabin jallabiyar fuskarta fayau ba wata kwaliyya ta azo a gani amma hakan bai hana bayyanar tsantsan kyan da Allah yayi mata baiwarsa ba. A hankali ta fara dago kanta ta na saukewa a in da ta ji maganar sosai ta ware idanu ganin wacce take gabanta cikin yanayi na mamaki da wani irin haushi da ya kasa boyuwa har sai da ya fito cikin idanuwanta gyaɗa kai tayi kafin ta mai da kanta kan Aikin ta. "Dr.Abdurrazaq Erena". Abin da ta fadi kenan tana mai wani kara bayyanar da wani murmushi dake fuskarta wanda kallo daya zakayi masa ka san ba a so ba. Ba tare da ta dago da kallonta ba murya kasa kasa. "Hawa na biyar hannunki na dama office mai lamba Uku". Ba ta tsaya ansa ta ba ta dauko kafafuwanta ta fara tafiya a haka har ta hau Abin da zai kaita wajan cikin yan sakanni ta isa bayan ta sauka ta kalli kwatance da kayi mata wata kofa glass ta hango sannan ta kalli samanta murmushi ta saki ta fara takawa a hankali ta isa sakatariya ta gani zaune tana ta faman aikinta hankali kwance kwankwasa kofa glass din tayi kadan tana mai kallonta cikin wajan a hankali ta dago kai ita ma ta sauke a kanta murmushi akan fuskarta lokacin da ta dago amma tana cin karo da wacce ke gabanta ta tsuke fuska hadi da jan guntun tsaki tana kau da kanta. Sai da ta shafe sakanni kafin tayi mata alamun ta shigo a hankali ta taka ta shiga ta dan yi kasa da glass dinta ta shiga motsa laɓɓanta. "Please wajan Dr. Abdurrazaq Erena nake bukatar zuwa". Kallon ban gane ba sakatariyar tayi mata tana mai kwaɓe baki kafun ta kau da kai hadi da fadin. "Ya san da zuwan ki ne?". Shiru tayi ba tare da cewa komai ba na yan dakiku hakan ya kullar da sakatariyar da sauri ta shiga duba cikin kwafutar dake gabanta tana yawatawa da idanuwanta cikinta. "Duk yau a cikin jerin mutanan da za su zo gare shi ban ga alamun da ke a ciki ba". Ta fadi tana mai dago kanta ta saukewa gareta. a dan harzance ta sauke glass din ta sosai idanuwanta kan sakatariya kallonta take yi tana karantar yanayin da alamun so take ta samu wani tangarɗa da zata jona mata amma cikin nuna na fiki. "ki je ki ce masa Areefa Saifullah ita ce take son ganin sa ya san da zuwana". Yanayin yarda take maganar a dake da yanayin bacin rai ya sanya sakatariyar ware idanu sosai gami da tallaɓe haɓa tana kallon yarda wannan mai kalar gangar ke mata magana akai. A hankali ta mike saman kafafuwanta masu sanye da wasu takalma masu matukar tsine kamar za su karye a hankali ta fara taku da dan guntun suket dinta wanda iyakarsa guiwa kadan taɓe baki Areefa tayi tana bin dumemiyar matar da kallo wacce tayi biyunta. Mintina kalilan sai gata ta dawo tana faman tsuke fuska. "ki Shigo kofa ta uku ita ce in da yake ciki". Gyaɗa kai kawai tayi gami da wucewa tana taku ko ina na jikinta rawa yake yi lokaci guda ta canza tafiyar da take yi ita dai sakatariya sakin baki tayi tana kallon ikon Allah har sai da Areefa ta bace mata sannan ta saki ajjiyar zuciya ta koma ta cigaba da aikin da take yi. "Areefa Saif...". Abin da ya fadi kenan yana hanzarin mikewa cikinsa har ɓari yake yi ya zagayo izuwa in da take tsaye hannunta rike da Handle din kofar sai faman yawatawa da idanuwanta take yi cikin Office din har ya iso ya tadda ita nan tsaye sai faman sakin wani murmushi yake yi hakan ya bayyanar da wawulan hakorin sa daya na gaba da ya cire amma in ba ka gane ba sai kayi zaton wushirya ce ta buɗe sosai a jerin hakoransa masu dan duhu kadan. "Ban yi zaton ai yau zaki zo ba, domin Alhaji Abdulwahab ce mani yayi sai nan da gobe". Ya fadi har lokacin idanuwansa na bin duk wani sashi na jikinta yana kallo kafun ya yi mata nuni da kujerun dake cikin office din alamun taje ta zauna sosai take kallonsa ta cikin glass dinta tana karantar yanayinsa sosai take hango komai kamar ma ya yuwu kallonsa take yi tun daga fuskarsa har kafafuwansa babban mutun ne don a kalla zai baiwa shekaru hamsin baya amma hakan bai nuna a fuskarsa ba saboda yanayin huta da jindadi da suka taimaka ma jikin nasa baki ne amma ba can ba yana da idanuwa masu dan girma sun dan yi ja kadan hancinsa ba dogo bane yana da fadi haka ma bakinsa mai dauke da manyan laɓɓa masu kalar baki baki haka zai tabbatar ma da yana shan wani abu. Ba tare da ta ce da shi kala ba ta doshi cikin Office din sosai tana wata irin tafiya ta firgita duk wani namiji da yake gabanta har ta isa ta zauna ta ajje jakar dake hannunta gami da daura kafa daya kanta daya a hankali ta sauke glass din dake fuskarta gabadaya shima ta ajje shi kan Table din dake gaban kujerun ajje numfashi tayi alamun gajiya gami da dan dafe kai. A hankali ya fara takowa in da take kallo daya zakayi masa kasan sosai Areefa ta tafi da guntun imaninsa jikinsa sai ɓari yake yi fuskarsa tana sakin murmushi idanuwansa kamar za su fado kasa. "Areefa Saif...". Ya sake fadi cikin salo na yin kasa da murya kamar wanda yake rokon wani abu a gareta. Kaɗa idanu tayi gami da dan daga girarta tana mai yawatawa da idanuwanta akan sa zuciyarta nayi mata wani tsalle na murna da jin wani dadi amma bata bari hakan yayi tasiri a fuskarta ba domin a gimtse take ba alamun dariya. A hankali ta fara motsa laɓɓanta da wani irin yanayi tana mai kaɗa idanuwanta. "Ya kamata ace ka koma ka zauna domin time dina a tsare yake akwai in da zan je ne". Ta fadi tana da murmushi a fuskarta da sauri ya ja gefe gami da ware idanuwansa sosai ba tare da yace komai ba ya koma can inda kujeransa take mai juyawa ya zauna gami da saka kan biro a bakinsa yana cizawa kujerar na watayawa dashi idanunsa akanta sai faman sakin murmushi yake yi a hankali ta kau da kai gami da tura masa fiyal din da ta zo dashi. Hannusa guda ya kai yana janyo fiyal din yana mai sauke idanuwansa akansa buɗewa yayi a hankali yana yawatawa da idanuwansa a cikin tsayin minti daya kafun ya mai da ya rufe ya dan bugeshi kadan ya dago kansa ya dubi Areefa wacce ita ma hankalinta na kansa ta na kallon yarda yake duba fiyal din. "Komai yayi daidai zaki iya fara aikin zuwa On Monday in kuma akwai Time din da kika zaba zaki iya amfani dashi...". Hannunta ta dan daga kadan tana dan murmushi. "No ba ni da wani lokaci sai wanda ka yanke mani domin ina bukatar fara aikin ne akan lokaci ba tare da zabina ba sai zabin da kuka bani". Ta karashe tana mai mikewa kan kafafuwanta gami da daukar jakarta ta. "Ina Godiya". Ta fadi tana mai kara sakar masa murmushi shi dai idanuwansa har zuwa lokacin suna kanta kamar wanda aka jona wa mayen karfe har ta fara taku amma bai motsa ba motsin Handle din da ya ji ne ya fargar dashi da sauri ya ware idanu yana kokarin tashi amma ina kafun ma ya kai ga tashi ta fice daga cikin Office din komawa ya yi ya zauna jikinsa ba kwari hannu bibbiyu ya tallaɓe haba da su yana kallo kofar yana faman sauke numfashi a hankali. [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA GOMA SHA UKU. Kai komo kawai take yi a tsakar dakin ako wani takunta daya sai ta dubi Huzaif tana mai ajje numfashi sosai da sosai take jin haushinsa da takaici akan abin da ya aikata sosai take kallon abin a matsayin babban kuskure mai girma sosai a idanuwant sosai take ganin wautarsa da ganganci da kuma yada zuciya kare ya dauke. Numfashi ta ajje bayan ta tsaigata da kai komon da take yi sosai ta ajje ganinta akansa. "kasan kuwa abin da ka aikata kasan kuskuren da ka aikata ya girmama sosai a idanuwa...Well bana tunanin kai lamarin ka dauke shi a matsayin kuskure mai girma a idanuwanka". Ta fadi tana mai cizon laɓɓanta bayan ta turasu cikin bakinta sosai zuciyarta ke zafi da raɗaɗi akan komai da ya aikata sosai take jin abu mai nauyi ya tsaya mata a kirji ya samu gurbin zama sosai take jin tamkar ita ce akayi wa wannan cin kashin. "Bana tsammanin Huzaif din dana sani ne wannan bana tunani Huzaif din asali ne wannan anya kuwa ba wasu abu akan ka ba na tunanin abin da kake sha zai sanya ka aikata wannan kuskuren mafi girma a idanuwana". Ta sake fadi tana mai girgiza kai sosai take jin komai da ya faru yana dawo mana ina ma tasan hakan zata kasance da tabbas sai Mariya ta raina kanta kamar ta yarinya karama har tasan ta daga hannu ta mari namiji namijin ma Huzaifa. "Kaico!". Cikin wani irin sauti ta furta kalmar tana jin ɗacin lamarin ako ina na zuciyarta da ruhinta. Harɗe hannayenta tayi a kirjinta tana kallon yarda komai na Huzaif ya canza sosai take ganin lalacia tsakanin idanuwansa da zuciyarsa sosai take hango gazawa a gareshi kau da kai tayi domin in har ta cigaba da dubanda da ganinta tabbas zuciyarta zata iya bugawa don tsananin takaici. "Yaa Allah ta ya ya zan dubi wannan lamarin a wani MIZANIN HANKALI ya dace na ajje wannan lamarin bana tunani ko mai tabuwar kwakwalwa zai iya abin da ka aikata...". "KHAIRIYYA". Muryar Huzaif ce ta karaɗe dakin cikin wani irin sauti mai tsoratarwa cikin rashin tsammanin samun maganarsa ta ji ya ambace sosai ta saki zaren kalamanta ta saki baki tana kallonsa sosai take jin gabanta na bugawa gabadaya ganinta ta ajje a fuskarsa komai na shi take kallo da yarda tashin hankali da bacin rai suka nuna a filin komai nashi har zuwa lokain idanuwansa a rufe suke hannayensa saman fuskarsa sai faman juya su yake yi. "Excuse me. Please". Abin da ya sake fadi kenan idanuwansa a rufe tana kallon yarda laɓɓansa suke rawa sosai wajan furta ko wani harafi guda na kalaman da ya furta. "ki bar ni naji da abin da ke kokarin yayyaga mani zuciyata please ki barni naji da abin dake kokarin tafiya da ruhina sosai da sosai nake jin bani bane Khairiyya bana zaton ni Huzaif". Yanayin yarda laɓɓansa ke rawa da yarda kalaman nasa suke turereniya ga junansu hakan zai tabbatar maka akwai tashin hankali mai girma a zuciyarsa da ruhinsa wanda bai yi zaton wanzuwansa ba a duniyarsa sosai komai na tashin hankali ke bayyana kansa a ko ina nasa. Rintse idanuwa Khairiyya tayi sosai da sosai take jin wani abu mai nauyi na samun gurbi a zuciyarta sosai da sosai take jin zata iya daukar kowa ni tashin hankali da take hangowa cikin idanun Huzaif ba za ta iya daura ganinta ta cigaba da ganin halin da yake ciki ba ba za ta iya cigaba da jin numfashin sa mai cike da tashin hankali ba. A hankali ya fara kokarin daga dan yatsar sa dake fama karkawa sosai yake jin wani iri cikin zuciyarsa da inda take zaune a kirjinsa gani yake kamar wauta ya tafƙa sosai a duniyarsa amma ban yi amanar haka a zuciyarsa ba hango Mariya yake yi a matsayim wacce take kokarin kashe kan ta da kanta domin kuwa sosai ta dauka wa kanta fitinar da ba zata iya saukewa kanta ba sosai yakke ganin hauka cikin komai da take aikatawa sosai yake ganin rashin kunya da fitsara tsantsa cikin idanuwanta dole ya dau mataki ko ba komai ya koya mata rayuwar duniyar nan da yarda 'ya mace bata isa ta galaba akan ko wani ɗa namiji ba dole ta san waye HUZAIF ABDURRAZAQ. A hankali ya mike yana duban Khairiyya da ta zuba masa idanu sosai murmushi yayi gami da dauke kan sa. "You can go". Abin da ya fadi kenan ya fara daga kafafuwansa cikin wani irin yanayi mai cike da abubuwa marasa dadi ga zuciyarsa Toilet ya nufa har zuwa lokacin idanuwan Khairiyya na kansa sai faman suke numfashi take yi a sauri-sauri sosai take jin wani iri a zuciyarta sosai take hango abin da zai dauko mata tashin hankali ya ajje mata a rayuwa sosai take hango abin da zai hanata rawar gaban hantsi a duniyar Huzaif sosai take hango komai na wargaje. Numfashi take ajjewa mai dauke da abubuwa masu yawa da take zaton za su sayo mata tashin hankalin rayuwa a hankali ta daga jakarta zuwa kafatar tana faman gyaɗa kai kawai take yi tana tana jin wani abu mai nauyi na sakar mata a zuciya da duk wani gurbi na cikinta a hankali ta fara takunta domin ficewa daga dakin zuciyarta na wassafo mata abubuwa ma bambanta. ******** Sosai da sosai take jin wani irin tashin hankali na kokarin samun masauki a ko ina na sassan jikinta sosai take jin yarda kwakwalwarta ke kwala ihu akan tunanin da ya zo mata a bazata sosai take jin wani sauti mai kara sosai yana amsa kuwwa a kunnuwanta sosai. Bugun zuciyarta yake kara sauri sosai da sosai takun da take yi da kafafuwanta suke aika mata da wani lamari na daban wanda yake kara hargitsa tunaninta idanuwanta a rintse suke komai take hangiwa komai da komai da ya faru yake dawo mata baya kamar yanzu ne yake faruwa a gigice take ajje numfashi mai tauri a kokarin janyo mata ruhi zuwa waje. Bata san lokacin da tayi cilli da fakar dake hannunta ba ta sanya hannayenta zuwa kunnuwanta ta rufe su ji take kamar za su tarwatse dalilin sauti da ke musu sukuwa a ko wacce dakiƙa. "Yaa Allah!". Abin da ta furta kenan a kasan laɓɓanta cikin wani irin yanayi mai wuyar fassaruwa a gareta jin gina tayi da kofar da zata sadata da cikin dakin gabadaya taji kafafuwanta na kokarin gaza daukar gangar jikinta ji take yi kamar jikin ba nata bane sosai take hango fuskarsa tun ranar farko komai yake dawo mata har izuwa wannan lokacin sautin saukar marin da tayi masa take ajin yana samun wajan ajje sautinsa a bangarori masu yawa daga sassa na jikinta sosai take hango wautar ta cikin aikata wannan kuskuren mai girma da zuciyarta ke ganin tayi sosai take ganin girmar lamarin na kara girmama a zuciyarta da tunaninta. 'Mai ya kai ta, mai ya kai ta aikata wannan danyen aikin, ta ya ya ma haka ta faru gareta tun da take ba ta taba marin wani mai girma kamarsa ba ko da bai kai shi ba bata taba mai yasa tayi haka ina tunaninta ya kai ta lokacin ina zuciyarta ta cilla a lokacin mai yasa bata hana ta ba'. Gyaɗa kai kawai take yi cikin daukar tashin hankalin da taji yana kawo mata hari, ta tabbata ba zai yafe mata ba, ta tabbata ba zai rabu da ita ba, ta tabbata zai shigo duniyar rayuwarta. Ta ya ya ta wacce suffa zai zo mata? Tunani da zuciyarta ke ta hasko mata ke tana kara gigita mata kwakwalwa da lamarin da take kara girmamashi. Abu taji mai dumi na saukar saman kumatunta ko bata tabbata ba ta san Hawaye ne bayan HAWAYEN ZUCIYA da taji ma tana yi abin har ya kai ga bayyana dole ta firgita da lamarin ita Mariya ta mari wani wanin ma mai girma girman da ya dace ace ta ganshi ta daraja shi amma ina! ZUCIYA BATA DA K'ASHI. 'Akan mi akan wani dalilin zaki damu kan ki. Kina zaton in da ya cimma buri akan kudirinsa a kan ki tashin hankalin da za ki shiga mai ya girmema wannan ba kawai don mari har zaki bari tashin hankali ya yi girma mafi girma gareki karki yi sake har wannan kankanin abun ya hanaki abubuwa cikin rayuwarki'. Wani sashi na zuciyarta ne taje tana amayo mata sautin zantukan nan. Sosai tayi shiru tana nazarin kalaman sosai komai taji yana kokarin dawo mata daidai a hankali ta fara gyaɗa kai tana jin yarda zuciyarta ta cigaba da wanzar mata da wasu batutuwa masu girma a gareta. 'Shin in da ya keta miki haddi mi kik zaton zai faru dake a duniyarki' Numfashi mai girma ta ajje gami da buɗe idanuwanta gabadaya sosai take kallon kanta sosai take kallon yanayin kankatarta tana kara nasarin abin da ta aikata a hankali komai da zuciyarta take fadi mata ya fara tasiri sosai a kanta sosai da sosai zuciyar ta dake komai na tsoronsa ya kai sai dai abu daya da take jin sa a zuciyarta duk a dalilinsa sai dai bata dan me nene ba bata san a me zata fassara shi ba sai dai zata iya barin sa a matsayin 'Mala' har zuwa nan gaba. A hankali ta fara daga kafafuwan ta da taji sunyi mata nauyi kamar an daura mata wani abu da yai karfin girman jikinta sosai take kokarin amfani karfin zuciya tana jansu tana sanya hannayenta tana dauke guntayen hawaye da suka zobo mata sosai take takaicin zubarsu akan wani can wanda bai san darajarta ba mai san kimarta ba mai san martabar ta ba... "Mariya". kamar daga sama taji sautin muryar ya sauka a kunnuwanta da sauri ta ja kafafuwanta da take ja daƙyar ta ajje su waje guda ko ba a fada mata ba ta san waye hakan ya hanata juyawa domin adaidai wannan lokaci tana bukatar zaman kadaici ita kadai ba ta so ta sake daukar wani abu da zai so canja masa lissafin da take faman yi azuciyarta runtse idanu tayi jin takunsa na isowa gareta sosai take nuna rashin so wani abu a yanzu sosai fuskarta ta bayganar da haka. A hankali ya isa gareta hannayensa sarƙe a juna jikinsa sanye da wani lallausar boyel mai kalar fari anyi masa dinki babu wuyar rigar an mata aiki da jare mai kyallin gold sosai kayan suka dace da jikinsa kansa sanye da hula ita ma dai kalar kyallin Gold ne doguwa ya dan rangwafar da ita kamar yarda yarbawa suke yi fuskar nan tashi fayau ba zaka ce ya hau shekaru talatin a duniya. Sosai yake karantar yanayin ta da yarda ya hango damuwa dauke a fuskarsa sosai yaji rashin jin dadi a ransa ciza laɓɓansa yayi kafin ya gyaɗa kai. "akwai abin da ke damunki Mariya". Ya fadi yana sake kafeta da idanuwansa manya sosai take jin rashin son magana a daidai wannan lokaci amma ba za iya ajje Dr.Aqeel a matsayi marashin girma gareta ba tana jin sa sosai a ranta da irin ALHERI da yayi a rayuwarta. "Uhmm bakomai kawai dai...". "Mariya mana". Ya fadi cikin muryar mai sauti da rarrashi a cikinta. A hankali ta dago kanta ta dube shi na yan sakanni kafin ta kau da kai tana hango yanayin kulawa sosai cikin idanuwansa gareta tana hango yarda ya nuna alamun damuwa da damuwarta. "Baabana". Ta fadi murya na rawa yanayin da tayi maganar zai tabbatar maka kamar iyakar gaskiyarta ta fadi ko da dai ba karya tayi ba lamarin bacewar Baabanta cikin rayuwarta yana cikin sahun abin da take zaton ƙaddara zata kawo mata na rashin natsuwa. "Yaa Salam!". Dr.Aqeel ya furta cikin rauni sosai kafin ya daura hannunsa akai yana mai cigaba da cewa. "Please Mariya ya kamat ace ki na sanyawa zuciyarki natsuwa gami da kwakwalwarki ke fa karamar yarinya ce sam bai dace ace har kin fara cin karo da irin wannan lamarin ba a rayuwarki kwakwalwarki ba komai zata iya dauka ba tsorona kar damu tayi miki yawa sosai wani abun zai iya kama ki na rashin dadin rai Please Mariya Rayuwarki tana bukatar komai mai dauke da sauki". Yanayin da yake ajje furucinsa da rauni a ciki da kuma rarrashi sosai hakan ya taba zuciyar Mariya ji take yi kamar ta rushe da kuka ita a karan kanta ta san sosai take cikin SIRAƊIN RAYUWA sosai take ganin yarda rayuwarta ke zuwa a a hagu ita kanta ta dani komai na duniyarta ba mai natsuwa bane ta sani sosai da sosai ƙaddara ke dawainiya da ita a duniyarta. "Mariya komai zai shige in har baki dau komai da zafi ba, rayuwarki tana da muhimmanci ga rasu rayuka masu yawa sosai wasu rayuka za su shiga tashin hankali mai girma in har ba ki rangwantawa kan ki ba". A dan tsora ce ta dago tana dubansa sosai taji kalamsa sosai take fahimtar in da ya saka gaba rintse idanu tayi kafin ta buɗe su ta fara kokarin daga laɓɓanta. "Ta ya ya hakan zata kasance, ta ya ya zuciya zata iya daukar wannan lamari mai girma ta ya ya karamar kwakwalwata zata iya daukar wannan lamarin mai girma, bana tunanin zan iya amfanar da wasu rayuka a halin da nake ciki bana tunanin ƙaddara zata iya bani wannan damar bana zatom ƙaddara zata juya daga shafin da ta buɗe mana mai dauke da kaya mai girma na rashin kwanciyar hankali bana zaton hak...". A hankali ta rintse idanuwanta tana tura laɓɓanta cikin bakin ta sosai take jin abu mai nauyi yana samun gurbi a zuciyarta sodai take jin kirjinta na nauyi da girma a cikinsa. "Bana tunanin Mahaifin ki zai guje ku a halin rayuwar da kuke ciki. Bana tunani zai samu kwanciyar hankali don ya bar ki bana tunanin saboda gazawa ce ko halin da mahaifiyarki take ciki ya sanya shi bacewa daga rayuwark...". "Dr.Aqeel mai yasa kake cewa haka, mai yasa kake kokarin sanar dani abin da zuciya ta ba zata iya samun wajan ajjewa ba". Nisawa tayi tana jin yarda zuciyarta ke wani karfi a duk fitar kalma daya daga bakinta. "Mai yasa mai tsaya mun tafi tare ba, mai yasa da zai tabi bai tabbatar mani da in da zai je ba, mai yasa ya boye mani wani abu kuma ya san zuciyata ba iya dauka za tayi ba mai yasa ya tafi tsayin kwanaki fiye da arba'in ba tare da ya waiwayo mu ba ina jin zafi a zuciyata ina son Baabana sosai da sosai yarda baka zato ina bukatarsa kusa da ina ina bukatar kullum na dinga kallonsa yana wanzuwa a DUNIYARMU a kullu yau min. Ban so ya tafi wata duniya ba ta daban wacce ba musan a wani hali yake ba kullum tashin hankalin rashin sa kara girna yake yi a ko wani sashi na zuciyata". Yanayin yarda take ajje kalmominta sosai suke taɓa zuciyarsa zuciyarsa yake jin tana wani iri tana saukar da wani lamari mai nauyi gareshi sosai tausayinta ke kara samun gurbi a ko ina na zuciyarsa sosai yake jin ba zai iya cigaba da kallon yarda komai na muryarta da zuciyarta ke kara rauni ba. "Yaa Salam! Mariya kiyi hakuri don Allah komai zai zo karshe, kuma Mahaifinki zai dawo gareki na sani duk in da yake kuna ransa domin ku ne rabin rayuwarsa ko ina ya ajje kafarsa dole ya kasance tunaninku yana zuciyarsa". "Amma...". "Haba mana Mariya". Ya tare da sauri domin sam ba ya bukatar ya sake jin wani furuci nata mai rauni ya daki kunnuwansa. A hankali ya fara juyawa domin komawa Office dama ita ya fito dubawa sosai yake jin yarda numfashinta ke sauka a hankali har ya bar wajan. A hankali ta daga kai ta bashi da kallo sosai idanuwanta suka cika da kwalla suna kokarin zubowa bayan hannunta ta saka ta dauke su ta kwashe mintina a tsaye a wajan kafin ta kokarta jan jiki sosai take jin nauyi a ko ina na sassan jikinta musamman kirji don ji take kamar dutsen Dala aka daura mata kanta a kasa take tafiya sam bata lura da wanda ya ke gabanta ba sai da ya ga ta kokarin tureshi sannan yayi gyarar Murya a dan razane ta dago kai sau kadan ta bugi kirjinsa ta ja baya kadan tana mai jikin kunya sosai da sosai. Ya lura da haka Murmushi yayi kafin ya fara kokarin magantuwa duk abin da suke yi da Dr.Aqeel akan idanunsa komai ya faru sosai ya ji nauyi mai girma a ransa da zuciyarsa musamman yarda ya ji muryar ta na amon kalamai mausu dauke da rauniya da gazawar zuciya. "Mariya". Ya fadi a dan tausashe. Ba ta dago kai ba balle kuma ya saka ran amsawarsa ko da dai ba sosai yake bukatar amsawar ta ta don ya sani dole ya ji rauni a muryarta ko da kuwa ta amsa din shi kuma abin da baya so kenan a ransa. "Me ya sa?". Kan ta ne taji ya daure sosai da abin da ya fadi ba ta san ina furucin masa ya dosa bata san mai zata iya cewa a matsayin amsa gareshi ba ta san tambaya yayi amma kuma bata san mai ya dace ta fadi a matsayin amsa ba sosai take jin tsauri a furucin nasa sosai take jin komai na kwance mata domin ita dai ta san ba zata ce ga abin da ya dace tace dashi ba. Gyaɗa kai take faman yi sai motsa laɓɓanta take yi amma bata da abin cewa. "Na rasa dalilin da baki daukar shawara, zuciyarki sam-sam bata daukar abin da ake sanar dake, Me ya sa?". Sosai take jin nauyinsa a zuciyarta sosai take jin kamar bata kyauta masa ba don a yanayin da take jin furucinsa ya tabbatar mata kamar bai ji dadi ba. Amma kuma ba ta san dalili ba, ta san abin da yasa yayi wannan furucin ba, sosai ta fuskanci akwai abin da yake nufi da furucin nasa. A Hankali ta fara kokarin dago kai domin kallonsa amma tana jin yarda gabanta ki bugwa da sauri sauri a hargitse ta kalle shi idanuwansa na kanta sosai yake kallonta fuskarsa ba ta san a wata matsaya zata ajje taba. Bata hango haushi a ciki ba kuma ba ta hango fara'a ciki ba. A hankali ta fara daga laɓɓanta da taji sun mat nauyi sosai bayan ta kau da idanuwanta daga gareshi. "Hakuri...". "Bana bukata ni ba abin da kika yi mani, kuma ba abin da nake son ji daga gareki ba kenan". Yanayin da yayi maganar tasa sosai taji faduwar gaba don ta hango damuwa a cikinta sosai da sosai rintse idanu tayi ba ta so, ba ta so ko kadan ace ta dalilin ta mutum mai ALHERI ya shiga damuwa rashin kyautawa take hangowa a gareta. "Ban san mai zance da kai ba, ban san ina ka dosa da maganar ka ba, bani da abin cewa domin maganar taka sosai na rasa inda zan ajje ta kayi hakuri don Allah". Maganar ta ta tayi rauni sosai hakan ya sanya shi sassautawa a muryarsa don ya fuskanci kamar taji damuwa a maganarsa. "Ban so na shiga rayuwarki don ta kura miki ba, ban son abin da zai kara rikitar miki da tunani, bukatata kawai shine damuwarki a ranki ki rage ta sam! hakan bai da ce ba a matakin shekarun ki Mariya sosai take jin rashin dadi a rai na da lamarin daukar ki nake kamar kanwata ban son abin da zai dinga saki damuwa bana jin dai har kasar ruhina". Hannayensa ya yarfar cikin yanayi na rashin jindadi kafin ya sake cewa. "ki shiga ciki don Allah ki wutar wa ranki Umma ta tashi na bata magani haka Mu'azzam ya faka amma ya koma don haka ba abin da za kiyi yanzu illa ki zauna ki ragewa kan ki tunani in kuma kina da abin yi ki je kiyi don karki zauna kuma ki fada wata duniyar ta tunani na san halin ki Please Alkawari". Ya karashe cikin muryar rarrashi sosai da sosai taji wani iri a ranta hakan ya haifar mata da kasa mai yawa daga cikin abin da ke damunta a rai. Kanta a kasa ta wuce shi sumui-sumui kamar maras gaskiya sai da ya ga shigewarta sannan ya saki ajiyar zuciya mai cike da tausaya kafin ya saki murmushi don ya lura ta amince da abin da yace kuma za tayi din rufe idanuwansa yayi na yan sakanni kafin ya buɗe su fuskarsa da fara'a kamar koyaushe ya fara taku domin ficewa. [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA GOMA SHA BIYAR. Sosai yake jin rashin natsuwa da kwanciyar hankali suna samun waje a filin zuciyarsa. Sosai yake jin wasu abubuwa masu kama da kibiyar ajali ga zuciyar na sassoke masa kirjinta. Sosai yake jin duk wata natsuwa tana fallewa da gudu daga filin rayuwarsa ta duniyarsa. Komai tafe yake da tashin hankali a yanzu cikin duniyarsa sosai yake tsammanin ba shi da wani farinciki a rayuwarsa cikin rashin zato da tsammani yake kallon komai na rugujewa a duniyarsa na farinciki kamar tubalin toka. Sosai yake jin zuciyarsa na zafi da raɗaɗi in ya tuna abin da faru dashi kwanakin baya sosai yake ji kamar zuciyarsa zata yayyage daga kirjinsa yana jin yarda kunci ke wanzuwa a duk tuni da yayi akan abin da ya faru dashi sosai yake jin wani makaƙi mai daci daga makogoronsa har saman harshensa. "Mu'iz ban san abin da yake damu na ba, ban san abin da ya ke kokarin dauke min farinciki da walwalar duniyata ba sosai komai ya ke kwance mani sosai nake jin bacin rai a cikin kokon zuciyata da ruhi...". Sosai yaji wani nauyi mai girma ya na samun mazauni a kirjinsa gami da saman harshensa gabadaya yaji maganar da yake kokarin karasawa ya kasa hakan laɓɓansa wanda suka dan bushe kadan ya tura cikin bakinsa yana cizawa hadi da rintse idanuwa ji yake yi kamar ba gaske ba gani yake yi kamar a mafarki ne komai ke faruwa dashi bai taba kawo wa kansa ƙaddara mara armashi zata fado masa ba ya yi zaton shi mai sa'a ne a duniyarsa dama rayuwarsa baki daya. A hankali ya dago kansa dake sunkuye hannunsa rike da igiyar shisha da ya gama bankawa cikinsa a tunanin sa zata dawo masa da duniyarsa kamar da a tunaninsa komai zai wuce kamar ba ayi ba a tunanin sa za tayi masa maganin matsala ko ma yace matsalolinsa da suka tokare masa duniyar farincikinsa amma abun ya ci tura. Nisawa yayi sosai har sai da kirjinsa ya harba. "ba zan iya ce maka ga kwanakin da na dauka cikin wannan yanayin ba amma dai zan iya tuna ranar. Ranar da takasance mani SANADI ga duniyar natsuwa ta ranar da ta kasance mani tamkar BAKAR RANA mai cike da kwazazzaban tashin hankali...". Nisawa yayi sosai yana kokawa da numfashinsa ji yake yi yana yawo dashi a wata duniya yana kokarin barin gangar jikinsa. Mu'iz da ya tallabe haɓa idanuwansa kan Abokin nasa yana kallon yarda yake sauyawa lokaci guda mamaki abin yake bashi yarda yake ganin tashin hankali da wani abu wanda shi kansa bai san menene ba cikin idanunsa a hankali yake gyaɗa kai yana kara gyara zaman hannayensa a haɓarsa. "Ban san in da bahagon zancen nan naka ya dosa ba ya kamata ace ka fito ka fada min dalili ba wai abin da kake ji nake so ba a'a yarda akayi komai naka nake ganin yana canzawa lokaci guda Me Ya Sa?". Ya ida yana mai yawata idanuwansa kan abokin nasa sosai so yake yi yana hango wani abu wanda zai bashi karin haske akan lamarin amma sam bai gani ba sai tsagwaron tashin hankali da yake cikin idanuwansa da suka kaɗa sukayi jajir matuka. "Mu'iz me ya sa ka kasa fahimta ta ya kamata ace duk wannan furucin da nake yi ka san in da na dosa ba wai ka nuna halin-ko-in-kula ba". Ya fadi yan gyada kai fuskansa na kara bayyanar da kuncin da yake ciki sosai zucyarsa ta fara kwaso masa wani lamari tana ajjewa a kokon kansa cikin mazaunin tunaninsa. To da yake wannan hayagagar yace wa Mu'iz me mai zai ce masa me zai ce masa dalilin kuncinsa shi sai yanzu yake ganin wautarsa kamar yarda Khairiyya tace dashi taga rashin wayonsa da dabara akan wannan lamarin ba ta san abin da yasa yake zuzuta kankanin abu irin wannan ba wanda shan ruwa ma ya fishi sauki matuka. Girgiza kai ya shiga yi yana jin wani sashi yana kambama lamarin sosai wanda hakan yake kara masa kunci a ransa da ruhinsa sosai yake jin wani hali na daban mai dauke da tsanani musamman in zuciyarsa ta bankado masa abin da ya faru gami da sunan da yake ji a ko wani sakan yake amsa masa kuwwa yake kara haifar masa da wasu abubuwa a zuciyarsa da ma gangar jiki baki daya. "kai nake sauraro". Mu'iz ya katse masa tunanin da ya afka ciki yake yawata dashi wata duniyar ta daban. Mikewa yayi daga cikin kujerar da ya cusa kansa ya saki igiyar shisha tayi kasa hannayensa duk biyu ya cusa cikin cikakkinyar suman kansa yana cakuɗawa gami da yatsine fuska kamar zai fashe da kuka a hankali ya fara taka kafafuwansa yana yawatawa cikin dakin idanuwansa a rintse sosai kafin ya sake buɗe su ya sauke kan Mu'iz wanda shi ma idanuwansa na kansa. Ba wanda ya sake kokarta cewa komai cikin su tsayin lokaci mai nisa iyakar nazarin Huzaif ya kasa samun abin da zai ce da Mu'iz wanda shi yake damunsa haka shima Mu'iz din yayi shiru ne domin jin abin da yake dawainiya da abokin nasa amma da alamun bashi da niyyar furta ko da kalma daya ce. ***** "Sosai da sosai zan yi kewarki nan da yan kwanaki Mariya". Dr.Karami ya fadi hankalinsa da idanuwansa na kan Mu'azzam dake hannunsa yana yi masa wasa shi kuwa sai bangale baki yake yi. Wani iri bugu Mariya taji kirjinta yayi wanda hakan ya haifar da tsayuwar abin da take yi sosai taji numfashinta yana sama da kasa kamar zai fice daga jikinta bakinta ta dan buɗe kadan daga sunkuyen da take domin samun daidaituwar numfashi ji take kamar numfashin da take shaƙa ta hanci yayi kadan gareta a hankali take juya fida din Mu'azzam da take wankewa cikin ruwan dake girke gabanta. A hankali kalaman Dr.Karami taji suna haifar mata da wani irin yanayi gami da narkar mata da duk wani kuzari nata sosai ta fara jin wani gumi na keto mata daga cikin hanyoyin gashin dake jikin ta laɓɓanta ta tura cikin bakinta tana cizawa kadan-kadan jin furucin take kamar cikin duniyar mafarkinta jin su take kamar ba a zahiri ba ciza laɓɓanta da tayi hakan ya tabbatar mata da eh gaskiya ce tabbacciya. "Ba ki so ko?". Ya fadi jin shirun nata ya yi yawa kallonta yake yi da duk kan idanunsa yana ganin yanayin da ta shiga ya tabbatar masa da haka din. A dan razane ta dago kai ta dube shi kafin ta mai da kanta kasa tana yawata hannayenta cikin ruwan dake gabanta a hankali take girgiza kai tana motsa laɓɓanta alamun tana son cewa wani abu amma ta kasa shima ya lura da hakan. "kawai shikenan ma tun da ba kya son tafiya sai ki zauna ke ma ki zama ma'aikaciyar asibiti ". Yanayin yarda yake ajje furucinsa fuskarsa dauke da murmushi zai tabbatar da tsokanar da yake yi mata. A karo na biyu ta sake dago kanta a dan razane kafun ta ware idanuwanta kadan akansa . "Uhmm...". Sai kuma tayi shiru tana juya harshenta cikin bakinta idanuwanta akan Mu'azzam wanda shi izuwa wannan lokaci ita yake kallo. "ko Bakya so?". Ya sake fadi da muryarsa dauke da dariya sosai yana kallon yanayin da take shiga wanda hakan ba karamin burgeshi yake yi ba sosai ya fahimci sanyin hali da rashin son magana irin nata sosai yake ganin magana tana yi mata matukar wuya in suna tare amma kuma yanayin ta da yanayin da take furta komai nata ba karamin tafiya yake da zuciyarsa ba ga ta dai ba wata babbar mace bane amma yanayin da da salon da take komai sai ka rantse wata mace ce babba wacce ta baiwa shekaru talatin baya. "Na fa gaji Malama in kin gama ki zo ki amshi Mu'azzam tun da na lura zaman nan din bai ishe ki ba". Ya fadi cikin murya mai sauti yana mai kau da kai fuskarsa dauke da dariya amma yanayin muryar da yayi amfani da ita sai ka rantse bacin rai ne a cikinta. Cikin hanzari ta mike jikinta har rawa yake yi zuciyarta na tsalle fuskarta lokaci guda tayi rauni sosai alamun ba ta so yanayin da ya nuna ba cizon laɓɓanta tayi muryarta a raunane. "Uhmm yi hakuri". Ta fadi dakyar tana mika hannu za ta amshi Mu'azzam gocewa yayi kafin ya juya ya kalle ta sosai yana murmushi. "Kin fiye tsoro da yawa ban san dalili ba kina da shariya Mariya mai yasa ko ni ne...". ware idanun da tayi akan sa ya sanya shi sauri yin shiru yana dariya kafin ya juya ya fara tafiya ba tare da ya bata Mu'azzam din ba. Sosai take ware idanuwanta akansa tana kallon yarda yake ajje takunsa a duk takunsa daya tana jin yarda zuciyarta da ruhi gami da gangar jiki ke amsawa kamar ita yake takawa da takalmar kafafuwansa sau ciki masu kalar ruwan kasa sai daukar idanu sukeyi da yanayin kyalli kirar kamfanin Gucci rintse idanu tayi sosai gabadaya taji tana juyawa kamar wacce aka saka a majanjawa take walagigituwa da ita ta dauki dakiku masu yawa a wajan kafun ta ware idanuwanta sosai wanda har zafi-zafi taji su na yi mata gyaɗa kai tayi gami da zubda ruwan da ta gama wankin fidar Mu'azzam ta dauki karikitan ta fara takun kan kafafuwanta a hankali kamar wacce kwai ya fashewa a ciki. Sosai tayi nisa cikin tunani kawai ajje kafafuwan ta take a duk in da taji sun sauka duk taku daya sai taji numfashin ta na janta tana kwato shi. "Mariya". Cak! ta tsaya kanta a kasa sosai taji muryar ta dakar mata kwanya gami da kara kawo mata wani abu na daban kuma zuciyarta lokaci guda ta buga. Kwanaki kusan uku kenan rabon da taji ko da muryarsa ta rasa dalili a zuciyarta tajima tana nazari anya ba laifi tayi masa ba ya dauke kafafuwansa yake guje mata ya daina son saka ta a idanuwansa sosai take lura da wasu halaye nashi na daban masu tsauri wanda a iya zaman ta dashi ta fuskanci haka mutum ne shi mai saurin fushi ga zuciya abu kadan ne yake sanya shi janye jiki ga mutum. Takun da taji nasa yana tunkaro ta hakan ya kara sautin bugun zuciyarta ta shiga kokawa da numfashin ta ta san shi mai alheri ne kuma ta gani sai dai ta rasa mai yasa cikin lokaci kalilan take jin wani irin abu game dashi sam bata so su kasance tare domin kuwa halayensa da yake amfani dasu sam ba su dace da ita ba sosai take jin ba dadi bata son mutum mai tsauri da sauri fushi akan abun da bai taka kara ya karya ba. Ita dai a iyakar tsawon lokacin da suka dauka cikin asibitin nan daidai da rana daya ba ta tsammanin tayi abun da zai bata masa rai sai dai bata sani ba ko cikin rashin sani tayi masa ba daidai ba wanda sam bai kamata ace ya kama ta da laifi akan hakan ba. "Mariya". Ta ji ya sake kira wannan kiran sai dai ya bambanta dana farko domin taji muryarsa da wani irin sauti wanda ta kasa tattance shi. A hankali ta fara motsa laɓɓanta tana kokawa da numfashinta da taji yana sarkewa. "Na'am". Sosai taji hucin numfashinsa a kusa da ita a dan tsorace ta ware idanuwanta da suke kasa kafafuwansa ta hanga sanye da takalma ash-colour sau ciki sai faman daukar idanu suke yi a hankali ta fara dauko idanunta tana bin sa da kallo tun daga kasa jikinsa sanye yake da suit Blue mai turuwa sai farar rigar dake ta ciki nektayal dinsa kalar ash-colour yarda takalminsa suke hannunsa duk biyu sanye suke cikin ajihun wandonsa saitin idanunsa ta sauke nata ganin sosai taji numfashin ta yayi sama da kasa ya koma daidai amma duk da hakan bai daina tsalle tsalle ba wani abu ne mai girman gaske take hangowa cikin idanunsa wanda tajima tana ganin hakan amma na yau ya bambanta sosai da sauran lokacin can baya kamar wacce ya rikewa idanu sam ta kasa daina kallonsa idanuwansa sarke da juna duk da nashi na cikin farin glass wanda ya kara ƙawata fuskar tashi duk da dai akwai rashin fara'a a cikinta. "Uhmm...Dr.Aqeel...". Hannu ya daga mata ya wanzar da wani murmushi mai zafi a zuciyar mai yinsa girgiza kai yake yi kamar wanda aka fada masa wata magana da bai yarda da ita ba har zuciyarsa. "Bana bukatar jin komai Mariya na lura kin yasar dani daga duniyar ki sam-sam kin daina tuna ni a rayuwarki sosai ki ka zare ni daga cikin duniyar rayuwarki ban san dalili ba..Uhmm...ni dai na san ban yi laifi ba amma kuma naga an dauki fushi dani Me Ya Sa?". Sosai take jin maganganunsa na haifar mata da wani irin yanayi mai wanzar da daci a zuciya sosai take jin haushin kalaman nashi ya fiye son kan sa da yawa ta lura da haka domin duk cikin kalamansa ba abin da ke yawarawa sai son kai ba ta san dalilin da yasa Dr.Aqeel yake yi mata haka ba bata san me yasa yake kokarin canza matsayin da ta samar masa a filin zuciyarta ba sosai take ganin girmansa domin kuwa bata ta ba manta alherin da ya saka mata a duniyar rayuwarta ba ita da makusantarta ba zata taba manta yarda ya dauke su ya kai su wani matsayi ba a lokacin da wasu suke kin su suke jifansu da wulakantaccen kallo sun mai da su marasa yanci da martaba a idanunsu shi ne yayi kokarin ganin an daina kallon su haka ta sanadinsa komai ya wanzu amma ba ta san me yasa yake kokarin canza komai nasa ba cikin kankanin lokaci wanda ko da wasa ba ta taba zaton hakan ba a filin zuciyarta. Nisawa tayi gami da sanya hannunta guda tana dafe goshinta sosai take jin kanta na sarawa da duk wasu kalamai nashi sosai take jin rashin jindadin haka bata so zuciyarta ta canza mata matsayin Dr.Aqeel sosai da sosai take kallonsa a matsayin da take kallon Dr.Karami... Rintse idanu tayi wani abu mai girma taji ya danne mata zuciya yana kokarin karyata zancen da take yi a yanzu. Yaa Allah! Ta fadi a can kasan makoshinta wanda take jin sa yana wani irin bauri-bauri. "Ban san a wani matsayi kika ajje ni ba sosai da sosai nake ganin kin canza matsayin da nake dashi a idanunki da zuciyarki a can baya Me Ya Sa?". Ya sake fadi cikin wata irin murya wacce ta sanya Mariya saurin girgiza kai sosai take hango rashin adalci a furucinsa sosai take hango rashin dacewar hukuncin da yake yankewa a kanta sam! hakan bai dace ba ya kamata ace ya yi mata duba natsanake kuma ya ajje komai nasa na tunani a MIZANIN HANKALI kafun ya yanke mata hukunci sosai take ganin tsaurin hukuncin nasa wanda ta tabbata bai dace da ita ba. Gyaɗa kai ta cigaba da yi tana tura laɓɓanta duk biyun cikin bakin ta. "Dr.Aqeel bana zaton abin da kake fadi haka yake, bana zaton akwai adalci a wannan hukuncin da kake yankewa akaina. Ya kamata ace kayi nazarin komai sosai kake da matsayi na musamman a zuciyata ba zan manta alheri ba domin kuwa in har na mance alheri hakika na zama BUTULU wanda ba zan so haka ba". Yanayin da take furta duk kalma daya a furucinta tana faman rintse ido zai tabbatar maka da sosai take jin wani abu mai girma a zuciyarta wanda ba komai ya haifar da haka ba sai yarda lokaci guda take kallon mutumin da bata yi zato ba zai sauya daga yarda ta sansa a can baya. "Yaa Rabb!". Abin da ya fadi kenan yana mai ware idanuwansa akanta sosai yake kallon yarda laɓɓanta ke motsawa kalamai masu taushi suna fesowa daga bakinta yana kallon yarda take cijewa da raunin da yake kawo mata hari amma sai tayi amfani da jarumar zuciyarta wajan fadi masa abin da take ganin shi ne ya dace sosai da sosai. Gyaɗa kai yake yi yana faman yawatawa idanunwa a fuskarta dake fuskartarsa amma idanuwanta a dan kulle kadai wanda zara-zaran gashin idanunwan nata ya hana ya gane yanayin da kwayar idanuwan nata suke. Shirun taji yayi yawa har kafafuwanta na kokarin kasa daukar gangar jikinta a hankali ta dago idanuwanta ta sauke su fes akansa batare da ko ɗar! ba yanayin kallon da ta gani yanayi mata ya kara rura wutar bugun zuciyarta amma taki bari hakan yayi tasiri a zahirance cikin karfin hali ta fara motsa laɓɓanta. "Ban san abin da yasa kake kokarin daura min laifin da ban san dashi ba. Ban san abin da yasa kake kokarin canza komai ba. Kai kan ka kasani dole na damu da kai amma kuma kai na lura gabadaya ka sauya daga in da na san ka ban san dalili ba...Uhmm in laifi nayi maka kayi hakuri". Ta karashe fuskartar da wani murmushi wanda ita a karan kanta ba ta san yarda akayi ya samu gurbin zama a fuskar ta ta ba. Ta fara gajiya da tsayuwar da take yi ta lura sam! shi gajiya bata fara rauni a kafafuwansa ba a hankali ta fara taku akan kafafuwanta da take jin su kamar na roba ne suke kokarin narkewa amma karfin zuciyar da tayi amfani dashi ya hana hakan tabbatuwa. "Zuciyata...". Muryar Dr.Aqeel taji ta saki ihu da fadin haka wanda hakan ba karamin sakata cikin wani yanayi yayi ba matuka! Cak! Ta tsaya da takun da take yi lokaci guda taji wani irin abu mai kama da ruwa yana bin sassan jikinta yana haifar mata da wata irin kasala mai kokarin zubda ita kasa a hankali taja jiki ta isa kofar dakin da suke ta dafa ta sosai take jin duniyarta na juyawa da sauri-sauri kamar zata watsar da ita wani waje mai nisan gaske. Nisawa yayi yana kallon irin halin da ta shiga duk da jarumtar da ta sakawa kanta amma hakan bai hana wanzar da halin da ta faɗa ba nisawa yayi gami da cigaba da furucin nasa. "Sosai take tausayin ki sosai take son ta ga kina cikin farinciki mai armashi...". Nisawa yayi wanda hakan ya sanya Mariya sakin Gwauron numfashi ta ciza laɓɓanta. "Nasan da haka da dadewa shiyasa na baka matsayi mai girma a zuciyata kamar yarda kake fadi mani matsayina a gareka". Ta fadi tana mai yawatawa da hannunta saman kirjinta da take jin yana bugu kadan-kadan. Da sauri ta ja kafafuwanta ta fada cikin dakin bayan ta sakar masa wani yaƙe wanda take zaton wai murmushi ne tayi masa wanda ta karyata hakan. Sosai ya shiga gyada kai yana bin kofar da kallon kafun ya daga hannayensa duk biyun ya dafe kan sa da su yana mai faman juya kwayar idanunsa gami da ciza laɓɓansa. Bai san abin da yake kokarin faruwa dashi ba. Bai san mai yake koƙarin saka shi cikin wani hali ba sosai yake ji a ransa akwai abin da ke shirin faruwa dashi a zuciyarsa zuciyarsa ta jima tana sanar dashi amma ya kasa gasgata haka ya dauki hakan a matsayin hauka irin ta zuciya mai kwashe kwashe bai san mai yasa yarinyar nan tunaninta yake wahalar masa da zuciya ba sosai yake kokarin yakice komai amma hakan ya gagara ganin haka yake a matsayin wauta na zuciya sosai yake ganin rashin hankalinta sosai yake son kin amsa komai da take yi domin kuwa rashin dacewar haka ya ke gani a filin rayuwar duniyarsa. Ya kaucewa ganinta ko zai samu sassaci akan komai ya gujewa haduwarsu domin ko zuciyarsa zata daina yi masa wannan labarin kanzon kurege da kullum take masa ya daina wanzuwa in da take ne a tunaninsa haduwarsu ne ke haifar da haka ashe ba hakan bane domin kuwa rashin haduwarsu hakan ya kara rura wutar abin da zuciyarsa take kokawar kawo masa filin rayuwarsa wanda sam ya ki amincewa da haka wanda ita kuma zuciyarsa ta hakikanace abin da take sanar dashi dole ya yarda dashi domin kuwa shi kadaine zai sassauta masa komai na filin zuciyar tasa dama filin rayuwarsa gabadaya... Girgiza kai yake yina faman karyata zuciyarsa a hankali ya fara jan kafafuwansa da yake jin sun masa nauyi sosai, yana barin wajan domin ya lura zuciyarsa so take ta haukata shi da abin da yake zaton ba zai taba tabbatuwa ba har gaban abada... [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. *Ita gobarar zuciya ruwa ba zai kashe ba, so ne ginshikin halinta. ba kowa ke sani ba* --ISA AYAGI😘 BABI NA GOMA SHA BAKWAI. Abu mai girma taji ya zo mata wuya ya tsaya cak! Numfashi ma da kyar ta ke jansa don ji take kamar zata shiɗe a hankali ta kai hannayenta duk biyun ta dafe kanta da take ji yana kokarin tawatsewa sosai take jin kirjinta na buga a duk sakan sai take hango tashin hankalin da ta gan shi a ciki sosai take hango yanayin fuskarsa mai dauke da kayan damuwa masu girma sosai. Sosai take jin wani abu mai kalar tausayi yana saukar mata a wani sashi na zuciya yana haifar mata da wani yanayi mai sanya kasala da sanya wani wani ciwo mai girma. Ba ta san ya zata yi ba, ba ta san me take ji game dashi ba, ba ta san mai zuciyarta ke kokarin yi gareta ba, ba ta san mai yasa tunanin wannan mutumin yake kokarin samun waje a filin zuciyarta ba, ba ta san mai yasa komai ke kokarin wargaje mata da tunaninsa sa ba ta tsane shi bana ta son ko ganin fuskarsa a filin rayuwar duniyarta sosai take jin ɗaci da bauri a zuciyarta duk lokacin da ko sunansa taji sai taji kamar ta kurma ihu amma a halin yanzu wani irin yanayi take ji game dashi sosai KUDIRI da tayi akansa a zuciyarta taji yana kokarin rushewa sosai taji bangarori na sashin zuciyarta sun kasu kashi biyu suna faman tamka muhawara wanda hakan ba karamin sanya ta tashin hankali yayi ba wanda ita kanta ba ta san mai ya dace tayi ba, ba ta san mai ya dace tayi akan wannan lamarin na zuciya ba. A hankali take sauke hannayenta daga kanta idanuwanta take rintsewa tana buɗewa a hankali gani take yi komai da yake faruwa da ita a yau kamar mafarki ne ba gaskiya ba za ta so ace a cikin barci ne komai ke faru da ita za ta so ace ba a zahiri bane za ta so ace kamar tatsuniyar kanzon kurege ne wannan lamarin. Sosai take jin wani sashi na filin zuciyarta na halittar wani abu mai girma wanda yake kara tsuke mata da zuciya a duk sakan sosai take jin jikinta na samun wasu abubuwa da su ka danganci zuciyarta sosai take jin duk wani sashi na jikin ta na amsar abin da zuciyarta ke halitta ba ta san a yarda zata dauki abun ba bata san a wani irin ma'aunin hankalin ta zata ajje wannan lamarin ba komai take ji sabo na halitar kansa da kansa a zuciyarta da gangar jikinta. Nisawa take yi a hankali tana faman fizgar numfashi wanda take jinsa kamar yayi mara karanci sosai a gareta. A hankali ta fara kokarin tashi saman kafafuwanta tana jin yarda suke wani irin kokarin kasa daukar gangar jikinta sosai take ji wani abu mai sanya rauni a duk sassar jiki da zuciya yana samun gurbin zama a jikin nata. Safah da Marwa ta shiga yi cikin rashin tsammanin abin dake faruwa da ita ba ta san mai zata ce ba mata san wani irin tunani ya kamace ta ba bata san mai rayuwart take kokarin dauko mata ba ta jiho filin duniyarta bata san wani irin tashin hankali bane ƙaddara ke kokarin dauko mata a wannan lokaci zuciyarta! Sosai take ji kamar ba ta ta ba sosai take ji kamar wata zuciyar ce ta daban ta sauya a filin kirjinta. Komai take jin sa ba dadi sosai take jin saman harshenta na haifar mata da wani ɗandano mai bauri gareta sosai take jin zafin da zuciyarta da can kasar ruhinta suna kokari kwatar kansu a kansa. A hankali ta fara taku har ta isa inda Mu'azzam ke kwance idanunusa biyu da alamun farkawa tayi daga barcin da yake yi sai faman wasa da hannayensa yake yi yana kaiwa bakinsa yana tsotsa alamun yinwa yake ji. Sosai ta ware idanu akansa tana kallon sa mamaki ne sosai ya bayyana a gareta bata ji mptsinsa ba kuma da alamun ya jima da tashi daga barcin a hankali ta mika hannayenta ta dauko shi gami da rungumeshi sosai ajikin ta sosai take jin wani irin yanayi game dashi sosa take jin so irin na DANGANTAKAR YAN'UWANTAKA na ratsa ko ina najinta sosai take jin so dan'uwan nata a duk lokaci tausayin sa da jikan ke kara samun gurbi a filin zuciyarta na kara haifar mata da so mai tsanani game da shi idanuwata take saukewa akan nasa tana faman sakin wani murmushi wanda ita kanta ba ta san tayi shi ba shima Mu'azzam din murmushin yake saki don akwai shi da arhar dariya. "Ehem! Nikam ina jiye miki ranar da za ta zo ta kasance ta rabuwa da Mu'azzam ban san ya zaki yi ba?". Kamar daga sama ta tsinkayi muryar Dr.Aqeel na dukan kunnuwanta sosai taji wani irin faduwar gaba ta ziyarce ta a hankali taji takunsa na iso gareta sosai take ji a jikinta idanuwansa na kanta sosai take jin komai na jikinta ya zama kamar ba nata ba ita kam! ba ta san abin da ke dawainiya da ita ba a duk lokacin da Dr.Aqeel ya fado duniyar rayuwarta sosai take shiga wani yanayi na rashin gane kanta. A hankali ya karo ya ja kujera ya zauna yana fuskantar ta sosai fuskarsa kunshe da murmushi "Umma ba ta tashi bane har yanzu?". Ya fadi yana kai dubansa ga tsintsiyar hannunsa mai dauke da wani hadadden Agogo Gold-Colour kirar Rolex sai faman sheki yake yi yana kara wa hannun nasa wani irin kyau na musamman. "Uhmm ba ta tashi ba. amma... Ai kai kace sai nan da awa uku kuma naga daga lokacin da kayi mata allurar zuwa yanzu ba a ci awanni uku". Yanayin yarda take ajje kalmomin da take kokarin furtawa da laɓɓanta a hankali hakan ya shagalar da shi sosai komai cikin natsuwa da hankali take yin sa kamar mai tsoron kuskuren fadin wata kalma daya da bata dace ba gyaɗa kai yayi gami ya sake kai dubansa ga Agogon hannunsa. "Yaa Allah! Kin ga shaf! na mance Wallahi". Ya fadi yana fama yatsine fuska gami da dafe kai. Yanayin da yake nunawa sai ya sanya Mariya sakin baki tana kallonsa sosa take kallon yanayin da yake nunawa kamar karamin yaro sai faman turo baki gami yake yi yana cizon laɓɓansa. Ta gefen idanu ya kalle ganin yarda ta saki baki tana kallonsa sai ya cigaba da abin da yake yi don ya lura abin da yake yi din ne ya shagalar da ita cikin kallonsa sam bata lura ba tsayin lokaci har Mu'azzam dake hannunta ya kusan zuwa kasa cikin hanzari Dr.Aqeel ya kai hannayensa duk biyun ya tallebe shi wanda ita ma a daidai lokacin ta zabura ta kai hannunta domin gyarashi aiko sai hannayensa suka sarkeda na juna wani irin Shock ne gabadaya ya kama jikinsu da sauri Mariya tayi baya gami da sakar masa da Mu'azzam din idanuwanta a warwaje sai faman yarfe hannayenta take yi fuskarta na ya mutsewa kamar zata yi kuka. Yaa Salam!. Abin da ya fadi kenan cikin zuciyarsa da wani irin yanayi wanda ya kasa gane na menene sosai ya rungumi Mu'azzam amma har zuwa lokacin jikinsa bai daina sanar dashi Shock din daya ji ba. Bugun zuciyarta sosai ya kara sauri sosai take jin wani tashin hankali yana samun waje a jikinta da zuciyarta da can kasan ruhinta sosai take jin wannan yanayi mai ABOTA da bakon lamari wanda tun da take bata taba jin irinsa ba mutane da yawa suna sarkewa bisa rashin sani amma bata taba jin irin wannan yanayin ba. Wani fili na zuciyarta ya shiga sanar da ita:- 'shin kin manta waye kuka yi haka dashi. shin kin manta ɗa namiji ne kuma hakan sam bai dace ba mace da namiji su taba juna in har ba muharraman juna bane' Astagafurullah wa'atubu ilai! Abin da ta fadi kenan cikin zuciyarta wani irin tsoro taji ya game jikinta da sauri ta fara ware idanunta domin karantar yanayin sa bata fuskanci komai ba domin hankalinsa ma bai gareta yana can wajan Mu'azzam yana gyara masa kwanciya a jikinsa hakan da ta gani ya sanya ta samun natsuwa domin abin da zuciyarta ta fara hasaso masa ba hakan bane. "Amma dai yanzu Mu'azzam ya tashi ko. Naga yanayin barci game dashi". Kai ta shiga gyaɗa masa kamar yana kallonta domin ta kasa cewa komai bakin ta take jin yayi mata nauyi sosai tsoron magana take yi domin bata san mai zata ce ba jin jikinta take yi har yanzu shock din bai sake ta ba. A hankali ya dago idanuwansa jin bata ansa masa ba sosai yake kallonta ya ganin yanayin da take ciki sosai ta fahimci ita taji abin da ya ji a jikinsa sosai ya gane haka murmushi yayi kafun ya ce. "Magana nake yi fa ko akan Mu'azzam din masa sai an yi halin rashin son maganar?". Ya fadi har lokacin fuskarsa akwai murmushi ita ma wani yaƙe ta dauko ta daurawa fuskarta a tunaninta wai murmashi ta mai da masa kafun ta kokarta motsa laɓɓanta. "Uhmm yanzu ya tashi kai kuma.ka shigo". Ta fadi tana mai nuna kamar shine dalilin rashin yin komai akan Mu'azzam. Ya gane in da ta dosa don haƙa ya mike a kafafunsa yana kallonta ya mika mata Mu'azzam a hankali takai hannunta ta anshe shi. "Sai anjima". Ya fadi yana mai shafar kan Mu'azzam dake ta faman kallonsa yaka dariya. A hankali ya fara taka kafafuwamsa ya ficewa dag cikin dakin sosai yake jin wani irin yanayi a jikinsa sosai yake jin ranar yau a gareshi ta fita daban sosai yake jin yanayi mai zubi da wani yanayi mai armashi a jikinsa a haka har ya karasa ficewa daga cikin dakin. Wani ajiyar zuciya ta saki tana mai lumshe idanuwanta ta bude su akan Mu'azzam wanda ya kafeta da idanu kamar yasan abin da take yi ja masa kumatu tayi ya bangale mata baki sukayi hanyar Toilet din dake cikin dakin domin gyara masa jikinsa. ***** Tun ranar da ya hadu da Mariya ya sake jin filin duniyar rayuwarsa ya sake hargitsewa sosai yake jin ciwon da zuciyarsa take masa yana kara girma matuka gaya sosai yake hango tashin hankali mara musaltuwa na kara wanzuwa gareshi. Juyi yake yi saman gadonsa lafiyayye wanda yaji kayan shimfida amma duk da wannan taushin gadon da laushi da yake dashi hakan bai hana shi jin sa kamar akan ƙaya yake kwance ta take faman sassoke shia ko wani sashi na jikinsa. Bai sa mai ya dace ya yi ba, Bai san abin da ya kamata ace ya aikata ba domin ceton kansa, sosai yake jin kwanyarsa ta toshe gabadaya tunaninsa ya daina kawo masa abin kirki na a zo a gani. Zuciyarsa sosai yake jin tana kara ciwo mai girma a cikin filin ta sosai yake jin zafi da raɗaɗi a duk sakan sosai yake tsoron abin da zai faru dashi nan gaba in har zuciyarsa ba ta saman masa mafita ba sosai yake hango rayuwarsa gajarcewa take yi a duk sakan... handle din kofar dakinsa da yaji an kama ya sanya shi saurin buɗe idanuwansa da suke kulle yana.jin tunanin da yake ta faman yi na kanzon kurege ya tsaya cak!. Mu'iz ne ya shigo fuskarsa kawai zaka kalla ka gane akwai abin dake damunsa yanayin kallon da yake wa Huzaif zai tabɓatar maka akansa yake samun damuwa a filin zuciyarsa. "Ban san wata irin rayuwa kake kokarin rakitowa kan ka ba, Ban san mai yasa kake kokarin sanyawa kan ka abin da zai hanaka walwala a duniyarka ba, Ban san mai yasa ka kasa kokari wajan yaki da abin dake damunka ba?". Mu'iz ne yake fadin haka muryarsa cike da damuwa hannunsa harɗe a jikinsa ya jingina a kofar dakin ba tare da ya karo cikin dakinsa amma idanuwansa masu ciƙe da damuwa suna kan Huzaif dake ta faman juyi kan gadon gabadaya lokaci guda ya hargitsa shimfidar gadon. A hankali Mu'iz ke takowa saman kafafuwansa jikinsa na bayganar da yanayin sanyi da halin da abokin nasa yake ciki a haka ya iso bakin gadon ya zauna yana kallons sosai kafun ya kai hannunsa ya ja babban bargon da ya lullube kansa dashi jikinsa daga shi sai Boxer da singilet murɗanɗan jikinsa mai cike da kirar mazantaka sosai ya bayyana kau da kai Mu'iz yayi ganin yarda da yake ciki. "Ban san mai yasa kake haka ba ban san mai ka dauki rayuwa ba ban san mai yasa kake daukar abu da girma ba wanda bai dace sam ace hakan ba haba Huzaif mana". Ya fadi da rarrashi a muryarsa a hankali yake jan numfashi yana ajjewa kafun ya numfasa. "ji ka don Allah a hakan kake tunanin zaka cigaba da zama a Huzaif din da a ka san ka, haka kake tunanin zaka samu walwala a rayuwarka ba tare da kayi maganin abin da ke damun ka ba kana tunanin wannan halin da ka jefa kan ka zai maka maganin matsalarka kayi ganganci Huzaif...ba ma wannan ba sosai nake mamaki Huzaif da har zaka kasa fada min abin dake damun ka nayi mamaki a zuciyata yanayin da ka nuna ace abu na damunka amma a matsayina na abokinka shakiki amma ka kasa sanar dani gaskiya bakayi ABOTA adalci ba dake tsananinmu". Numfashi ya ja mai zafi kafun ya ciza laɓɓansa. "Ka tashi ina son magana da kai in kuma bani da wannan matsayin sai naji in san in da dare yayi mani". Yanayin yarda yayi maganarsa da muryarsa mai zurfi da zafi a cikinta ya sanya Huzaif motsawa yana faman cizon laɓɓansa a hankali ya ja jiki ya riko hannun Mu'iz. Da sauri Mu'iz ya kalle shi hawaye ya gani suna sauka a idanun Huzaif da sauri ya ware idanu ya na kallonsa yana mai kara rike hannunsa sosai. "Haba mana Huzaif! me nake shirin gani haka wai shin meke damun ka ne haka wai kuwa kasan yarda kake kuwa kana kallon kanka a MADUBI kuwa ka ga halin da ka jefa kan ka Huzaif Hawaye Huzaif hawaye a idanun ka By God Sake don Allah karka ce mani abun har ya kai haka kar kace mani matsalar da kake ciki har ta kai matakin da zaka zubda mata da hawaye...Yaa Allah!". Janye hannunsa yayi daga na Huzaif sosai yake ware idanunwasa yana jin yarda gabansa ke bugawa cikin wani irin mataki mai girma. "Ban san abin dake damu na ba, Mu'iz abu daya na sani Mariya ita ce ta dalilinta komai...". "Mariyaa!" Mu'iz ya fadi muryarsa da sauti sosai a cikinta da mamaki yake duban sa cikin wani irin yanayi wanda shi kansa bai san yarda zai fassara shi ba. "WACECE ITA?". Mu'iz ya fadi muryarsa da zurfi a cikinta yana mai kallon Huzaif da izuwa lokacin hawayen da yake zubda sun tsaya illa numfashi mai girma da yake ta faman ja kamar zai kufce masa. "Ban san ya akayi kudin ƙaddara ya rakito mani ita ba ban san mai yasa kaddara ta kinkimomin ita ba ta jeho cikin rayuwata ba sosai nake cikin tashin hankali mai girma Mu'iz ban san ya zan kwatatta maka yanayin da nake ji a zuciya ta ba abu ne mai girma nake jinsa ya samu gurbi a filin zuciyata wanda ban san menene ba ban taba jin irinsa ba koma.na taba ji ban taba jin mai girma kamar wannan ba". Zuciyar Mu'iz ce ta buga a hanzarce har sai da ya kai hannunsa ya dafe kirjinsa tsayin mintina masu auki kafun ya ja numfashi mai zafi ya fesar ya dubi Huzaif da yayi shiru numfashin sa sai kai kawo yake yi a hankali 'U'r in Love'. Mu'iz ya fadi a zuciyarsa da wani murmushi mai girma a fuskrsa kafun ya nisa. "Tashi ka zauna ka bani labarin yarda abun ya kasance". Mu'iz ya fadi fuskarsa da murmushi yana mai bubbuga bayan Huzaif sakato yayi Huzaif din yayi ganin yarda Mu'iz ya nuna masa a hankali ya ja jiki ya tashi ya zauna tsakiyar gadon har da tankwashe kafafuwansa hannayensa tallabe da haɓa ya warsa idanuwansa kan Mu'iz da shima idanuwansa na kansa sun shafe fiye da mintina goma a haka kafun Mu'iz yayi kokarin kau da shirun. "Bani labari mana Huzaif". Ya fadi yana kafe shi da idanu Sosai Huzaif ke kallonsa gabadaya ya rasa inda Mu'iz ya nufa sosai maganganunsa suka rikita shi ya rasa ina zai ajje su ya rasa ina suka nufa sai faman sauke ajiyar numfashi yake yi yana kallon Mu'iz "Ban gane ba Mu'iz me kake nufi". Ya tsine fuska yayi kafun ya gyaɗa kai. "Bani labarin wacece Mariya". tsura yayi da idanu yana tunanin mai zai ce da Mu'iz ta yaya zai ba shi labarin Mariya mai zai ce masa ya hada su kai ya shiga girgizawa yana cizon laɓɓansa a hankali shiru ya shiga tsakanknsu kafun ya kokarta sanar da Mu'iz yarda ƙaddararsa ta watso masa Mariya cikin duniyar rayuwarsa take kokarin rikita masa komai da komai. "Yaa Allah!". Mu'iz Ya fadi yana mai girgiza kai cikin wani irin yanayi wanda Huzaif ya kasa gane in da hakan ya dosa. "Ban san mai yasa kake haka ba ban san mai yas kake rayuwa haka ba ban san yaushe zaka yi wayo ba a rayuwarka ba ban san mai yasa kake daukar rayuwar duniya a abun azo a gani ba". Kau da kai Huzaif yana mai yatsine fuska don ya lura da inda maganganun Mu'iz suka dosa. "Mtss". Ya ja dogon tsaki kafun ya dubi Mu'iz a karo na ba a dadi. "ni ba abin da nake bukata ba kenan so nake ka samo mani mafita ba wai wani zance na daban ba". "tsiya ta da kai kenan Huzaif ya kamata ace ka fuskanci rayuwa tun yanzu kai ga ka da son yin abu amma sam abin bai yi maka kyau". Cikin rashin fahimta yake kallonsa yana nazarin kalamansa. "Na rokeka ka rabu dani Pease I don like this at All wallahi ya kamata ace ka gane ni sosai izuwa wannan lokacin...Mtss". "Huzaif you sport to no u'r in love...Yaa Allah abu kamar almara ban san ya zan fassara maka ba halin da kake ci amma dai akwai alamun so tattare da kai...". Ihu Huzaif ya fadi yana mai kaiwa Mu'iz wani wawan naushi a fuska da sauri ya kau ce cikin hanzari yana mai tashi daga kusa dashi cikin yanayin mamaki da kuma murmushi a fuskarsa shi dama ya san sa haka ta faru. "U'r so stupit Mu'iz baka da hankali wallahi na lura kana hauka sosai Yaa Allah ni kake wa wannan maganar kan uban ce...". Wani sarawa kansa yayi da sauri ya sanya hannu ya dafe yana mai yatsine fuska yana jin yarda zuciyarsa ke raɗaɗi da zafi. "Please I beg u in the name of Allah to leave me alot I don't wanna see you please and please...". Kansa ne ya sake dauka wata irin jiwa yaji tana sama da kasa dashi da sauri ya koma ya kwanta yana tattare jikinsa waje daya kamar mai jin sanyi sosai yaji numfashinsa na kokarin kwace masa wani irin tashin hankali yana zuciyarsa ta bankado masa lokaci guda gabadaya yaji duniyar na sukuwar doki dashi sosai yake hango tashin hankali ta yaya hakan za ta faru ta yaya Mu'iz zai kawo masa wannan mahaukacin tunanin nasa ya fada masa yace hakan ce take faruwa dashi ina! ba zai taba yuwuwa ba ai wannan hauka ce da rashin hankali kamar shi Huzaif ace wai son ta yake yi kaicon wannan mummunar labari. Wata irin zabura yayi ya dire daga kan gadon ya isa gaban Mu'iz dake tsaye kamar wanda aka dasa mamaki ne ya cika shi ganin yanayin da Huzaif ya nuna game da maganar da yayi masa wanda in da yasan haka ce zata faru ba zai fada masa ba. wuyar rigarsa da yaji an shaƙa ya sanya shi katse tunanin da yake yi da zuciyarsa. "Ban san baka da hankali ba sai yau, Ban san kwakwalwarka ba ita kadai bace akan sai yau, ni zaka kawo wa wannan takaicin da bakin cikin rayuwata ashe dama ba so na kake ba ashe dama zaman tsana muke yi tsakanina da kai Well..Well ban yi mamaki ba Mu'iz dama ance makashinka yana nan tare da kai ba tare da ka sani ba yau ka nina min true colour din ka kuma na gani". Yanayin yarda yake maganar zai tabbatar maka ba ya cikin hayyacinsa idanunsa gabadaya sun canza kamar ba nasa ba sosa jikinsa ke rawa hakan da Mu'iz ya gani ya tabbatar masa Huzaif ba ya cikin natsuwarsa yake wadannan sambatun masu kama da mai hauka tubaran dole yayi masa zuri'a domin ba ya cikin tunaninsa a hankali ya sa hannunsa ya zare na Huzaif dake wuyansa a hankali ya ja shi ba tare da gardama ba har ya isa dashi kan gadon ya kwantar dashi yana mai jama masa bargon ya lullubeshi sosai jikinsa ya wanzar da wani irin zafi sosai yana faman karkarwar sanyi sai jan numfashi yake yi da sauri sauri [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA GOMA SHA SHIDA. Juyi kawai yake yi kan kafcecen gadon sa yana faman kai komo da zuciyarsa da ta hana idanuwansa barci ko na yan mintina ne yayi iya yin sa amma abun ya ci tura sosai yake ganin komai na dawo masa kamar yanzu fuskarsa yake hangowa tana yi masa shawagi a cikin idanuwansa in ya rintse guntun murmushin da ta sakar masa a waccan lokacin yake hangowa na yi masa barazana sosai yayi nisa cikin tarkon ta da yake tsammanin ta ɗana masa ba wai aiki kawai ta zo nema kamfanin sa na AFC ba har da da faraunatar zuciyarsa wacce cikin dakiku ta zabare masa ita ta tafi da ita bai sai hakan ya afku ba sai cikin wannan sulusun daren wanda ya dace ace yana kwance yana barci domin baiwa zuciya da gangar jiki hutu amma ina! hakan ya gagara. A hankali ya kai hannunsa wajan makunnin wutar dakin ya kunna haske ya gauraye dakin agogonsa kirar Rolex da ke ajje saman yar karamar dirowa dake girki gefen gadonsa ya dauko ya duba karfe 3:15am. ya nuna masa sosai ya ware idanunsa yana jin yarda kirjinsa ya buga kadan maidawa yayi ya ajje sannan ya juya gefen hannunsa na hagu kafun ya dan tashi kadan ya jingina da fuskar gadon sosai hannu bibbiyu ya tallaɓe haɓarsa abun duniya yake ji duk ya addabar masa rayuwa ya surkutar dashi cikin yan awanni da ba su haura goma sha tara bs komai ganinsa yake yi kamar wanda akayi shekara goma sha tara kafun ya tabbata sosai yake jin wani iri a duk wani sassa na jikinsa da zuciyarsa sosai yake hangowa kansa tashin hankali in har abin da zuciyarsa ke sanar dashi bai tabbata ba sosai yake ganin komai zai iya faru in har Areefa Saif ba ta bashi dama ba. Zuciyarsa yaji ta fara yo masa kuwwa da zancen amincewa daga bangaren Areefa tana mai sanar dashi in dai da kudi komai zai kasance kamar yarda ya fuskanci ita kanta Areefa din zata so jindadi da hutu kamar yarda hakan ya nuna ba tare da yaji daga gareta ba. Ba ya zaton zai samu matsala in dai ta bangaren kudi ne tabbas za suyi masa abin da yake so kuma a lokacin da yake so ko tattama ba zai yi ba yana da kudi yana da kadara wacce zai iye sayr zuciyar Areefa da komai nata da ta mallaka ya zama dole ta yarda dashi ya zama dole ma ta amshi bukatarshi hannu bibbiyu ba tare da tsaya yawo da hankalin sa ba. Gyaɗa kai ya shiga yi yana hada hannayensa waje daya yana lakwasasu suna ba da wani sauti mai amsawa sosai yake sakin murmushi mai karfi a fuskarsa sosai yake jin wani farinciki na samun gurbi a filin zuciyarsa sosai yake hango amincewar abin da yake bukata daga Areefa sosai yake ganin yarda ta amshi bukatarsa cikin lokaci kalilan ba tare da ya samu wata tangarɗa ba gareta. A hankali ya koma ya kwanta yana kai hannunsa wajan makunnin wutar yana kashewa rufe idanunwansa yayi har lokacin fuskarsa bata rabu da murmushin da yake yi ba sosai yake hango Areefa a wannan lokacin tana yi masa shawagi a duniyar idanuwansa da suke rufe sosai yake hango wani tattausar murmushi na samun gurbin zama a fuskarta tana jefa masa wani kallo wanda yake kara rugurguza duk wani sashi na filin zuciyarsa yana jin yarda wani abu mai girman gaske yana wanzar da mazauni a filin zuciyarsa ta shi, sosai yake ganin rashin samun Areefa tamkar rasa rayuwarsa sane da duk wani buri da kudiri nasa da ya kafa akanta gani yake yi in har ya rasa abin da yake bukata a gareta tamkar yayi wa rayuwarsa babban gibi ne wanda ba ya tsammanin yana da abin da zai cike masa wannan gibin. Cikin wannan yanayi barci barawo ya zo yayi awon gaba dashi ya jefashi wata duniya mai dauke da Areefa a cikinta... **** A hankali ya shiga rage sautin wakar 'Don't Judge Me' ta Chris Brown dake tashi cikin sifukun motar wayarsa dake hannunsa ya shiga latsawa a yan sakanni ya kai ta zuwa kunnansa yana faman jan numfashi kamar wanda yayi gudun tsira sosai fuskarsa ke bayyanar da halin da yake ciki na damuwa sosai kunci ke wanzuwa a fuskarsa da kwayar idanuwansa. Laɓɓansa yake turawa cikin bakinsa ya na cizawa kamar ba a jikinsa suke ba sosai yake jin wani irin yanayi da zuciyarsa take haifar masa a duk sakan daya na jan numfashinsa. A hankali ya sauke wayar fuskar na kara ya mutsayewa cikin yanayi na damuwa da rashin abin yi sosai yake jin komai na kwance masa sosai yake jin lissafin kwanyarsa na wargajewa cikin yan dakiku bai san abin da ya dace yayi ba, bai san me nene ya kamata ace yayi ba a daidai wannan lokacin ba yana bukatar mataimaki yana bukatar wanda zai tayashi zaman jajen zuciyarsa daga halin kuncin da take ciki... Kamar wanda aka zungura da sauri ya sake dauko wayar da ya ajje gefe cikin yan dakiku ya kai ta kunnansa bayan ya binciko lambar da zai kira. A hankali yake jan numfashi yana motsa laɓɓansa zuciyarsa yake jin tana wani irin mataki da ya tabbata gaf take da kamuwa da cuta mai girma gareshi dama gabadaya gangar jikinsa. "Khairiyya...". Ya fadi cikin wani irin sauti mai rauni sosai a hankali ya sanya hannunsa daya yana dafe kansa da yake jin yana kokari wargajewa. Yana jin yarda numfashinta ke sama da kasa daga bangarenta sosai yake so ya fahimci wani abu cikin yanayin da take ciki zuciyarsa ta cilla shi wata duniyar tunani ya shiga nazarin yanayin da yaji Khairiyya sosai zuciyarsa take sanar dashi wani abu na daban da bai yi tsammani ba. Girgiza kai yayi cikin yanayi na kin yarda da zancen zucin nasa kafun ya nisa cikin yanayi na damuwar zucci. "Ban san mai nayi miki ba kika gujeni tsayin kwanaki Khairiyya, tun da nake dake daidai da kwana daya ba mu taba kin sa junanmu a idanuwanmu ba, amma cikin wannan lokacin gabadaya na lura sauyawa kike yi me yasa?". Ya ida muryarshi da sanyi a cikinta sosai yayi shiru yana jiran tsammani daga bangaren ta amma shiru kusan mintina biyu a hankali ya sauke wayar yana duba screen amma ba alamun yankewar wayar har yanzu akan kira take. "Uhmm...". Ya kokarta nisawa domin tunatar da ita yana kan layi in mantawa tayi take wata sabgar ta daban. Jan numfashi yaji tayi mai karfi kafun ta fara magana da wata murya wanda da ka jita zaka gane akwai abin da ke damun mai muryar. "Huzaif...". Ta fadi da sauti kafun ta sake jan numfashi ta dora. "Bakomai kawai dai...kawai gani nayi kana bukatar a baka fili a duniyar rayuwarka domin daidaita halin da kake ciki na damuwa...". Da sauri ya tare ta. "Haba mana Khairiyya wacce irin magana ce kike yi haka wanda sam bata dace ace ta fito daga gareki ba". Ya karashe yana mai jan numfashi sosai ya hasaso wani abu mai kama da bacin rai a cikin kalamanta sosai ya fahimci akwai abin da ke dawainiya da ita a zuciyarta. "Yi Hakuri...". "Huzaif!". Ta fadi da sautin murya mai nuna da bata so abin da yace ba. "me kayi mani kake bani hakuri, wanda ni ban sani ba?". "Ban ce nayi miki wani abu ba amma kuma muryarki ta fallasa asirin zuciyarki da halin da kike ciki". Yana jin yarda ta saki numfashi mai karfi kafun yaji maganarta ta doki dodon kunnuwansa. "bana gari nayi tafiya kuma gaskiya ban san ran dawowa nan kurkusa ba...". Bai bari ta ida batun nata ba ya tare da sauri. "What! me kike nufi Khairiyya kin yi tafiya ba tare da na sani ba mai haka ke nufi shin kin manta halin da nake ciki kuma kin san ina bukatar taimako daga gareki amma ki kayi min haka Well..shikenan..shikenan". Ya karashe cikin wani irin yanayi mai sanya daci akan harshe da zuciya Ita kan ta haushin nr cinkoshe a zuciyarta take faman kokawa dashi kar ya kufce ya yo waje domin ta tabbata komai zata iya gayawa Huzaif akan bacin rai da cin kashin da yayi mata. Sosai take jin bacin rai da takaici wanda ta hakikance haka a matsayin raini tsagwaron sa da rashin sanin darajar ta. Alkawari tayi sai ta bashi mamaki sai ta nuna masa asalin wacece ita sai ta ganar dashi 'YA MACE irin ta ba kowa yake dauka ya wulakanta ba sai ta nuna masa suma 'YA'YA MATA akwai daraja garesu ba wai ledar pure water bace duk in da ka gilma zaka tsince ta kuma ka zabi wanda tayi maka. "Sai Anjima!". Ta fadi a zafafe gami da kashe wayar bakidaya. Sakato yayi da baki bayan ya sauke wayar ya kafe Screen din da kallo wani abu yaji yanayi masa yawo akai ji yake yi duniyar na juyawa dashi a hankali komai na kwancewa akansa runtse idanu yayi mamaki ne da tu'aji yake kunno wa daga zuciyarsa sosai yake ganin kamar a mafarki wai Khairiyya ce tayi masa haka ita ce take fada masa magana cikin bacin rai abin da tun da suke da ita bata taba yi masa ba sosai take nuna kulawa da tattali gare shi amma a yanzu lokaci guda komai ya wargaje. Gyaɗa kai ya shiga yi yana hango rashin sa'a rayuwarsa wanda ƙaddara ta kinkimo ta kawo masa lokaci guda kuma take kokarin tarwatsa komai na ginin rayuwarsa da yayi a baya mai cike da kayan kwanciyar hankali da jindadi. Sosai ya jima cikin shiru hannayensa rungume da kansa zuciyarsa sai faman harbawa take yi da wani irin yanayi wanda ke kara hargitsa masa tunanin kwanyarsa sosai ya fuskanci rayuwarsa gaf take da tarwartsewa koma yace ya tarwatse domin kuwa shi dai bai ga amfanin haduwa da wannan yarinyar ba wacce ta dagula masa lissafi da komai nashi kuma take kokarin zautar dashi bai san abin da ya dace yayi mata ba bai san mai ya kamata ace yayi akan ta ba domin daidaituwar komai nasa sosai yake kasa aiwatar da niyyarsa gami da kudirinsa akan ta bai san mai yasa hakan na tunaninsa ya zama abokin sa a kowani lokaci dare rana dama cikin barcinsa ba wanda hakan ba karamin tashin hankali yake shigar dashi ba sosai ya fuskanci yarinyar ta samu gurbi a filin zuciyarsa tayi kane-kane ta hana zuciyarsa sak! da ruhinsa sosai take haifarsa masa da wani ciwo mai girman gaske a duk wani sashi na zuciyar tashi har da kasan ruhinsa. Numfashi yaja mai karfi kafin ya kai hannunsa saitin kirjinsa inda yake tsammanin nan ne zuciyarsa take girke wani irin bugu takeyi a hankali a hankali wanda hakan ya tabbatar masa ta kamu da ciwo mai tsanani har yake kokarin sumar da ita. Girgiza kai ya shiga yi yana jin yarda idanuwansa suke kokarin tara wani abu cikinsu wanda ko shakka ba yayi hawaye ne wanda shi kan sa bai san ya akayi har hakan take kokarin faruwa da shi ba da sauri ya sauke hannunsa yayi wa motarsa Key gami da kure karar sautin sifukun cikin motar yayi hakan ne ko zai samu sa'ida da saukin tunanin zuciyarsa sosai ya fizgi motar kamar zai tashi sama. ***** A hankali yake tafiya yana jin yarda kafafuwansa ke wata irin karkawa kamar za su fice daga jikinsa sosai ya ke jin tashin hankalin da zuciyarsa take hakilo akai kamar zai tarwatsa masa kirji sosai yake jin lissafin tunaninsa na kwanya na kara wargajewa. Bai san mai zai yi ba bai san abin da zuciyarsa take kokarin tunkuɗa shi yayi ba sosai ya barwa zuciyarsa gangar jikinsa take sarrafawa. "Yaa Allah!". Abin da ya fadi kenan a wahale kafun ya buɗe idanuwansa da yake jin su tamkar wanda aka daura musu wani abu mai girma sosai sun kaɗa suyi jajir. Mutum ya gani tsaye yana kallonsa sosai fuskrsa na bayyanar da wani irin yanayi wanda shi ya kasa fahimta shima kallonsa yake yi da duk ganinsa sosai yake jin zuciyarsa tana sanar dashi ya san shi ya taba ganinsa ko ba ma a zahirance ba zai iya kasancewa a cikin mafarki sosai ya cigaba da ware idanuwansa akan sa yana karaton a inda ya san shi lokaci guda zuciyarsa ta canko masa. Tabbas ya san shi sun taba haduwa kuma ko shakka ba yayi cikin asibitin nan ne suka hadu kwanakin baya can gyaɗa kai yayi kafun ya dan kauce gefe har lokacin idanuwan Dr.Aqeel na kansa sosai yake kallonsa yana karantar yanayin da yake yana kallonsa a ciki sosai ya fuskaci ba cikin hayyacinsa yake ba akwai abinda yake dawainiya dashi wanda ya kasance ba mai sauki ba ne. Daga kafada yayi kafun ya gyaɗa kai alamun ko a jikinsa a hankali ya fara taku kan kafafuwansa yana jin wani abu na samun gurbi azuciyarsa akan Huzaif sosai yake jin abu sosai yake jin gabansa na bugawa a hankali ya tsaya da tafiyar da yake yi ya waigo ya sauke kallonsa kan Huzaif har yanzu yana yarda ya bar shi sai hannu da yaga ya saka cikin sumar kansa yana cakuɗawa. Sosai Dr.Aqeel ke jin Huzaif bai kwanta masa azuciya ba sosai yake jin wani abu daban game dashi sosai yake jin abu mai girma na samun masauki game dashi tsaki ya dan ja kadan yana mai tsuke fuska, hada idanu sukayi tsakaninsu wani irin kallone ya sarke a idanuwansu kallo na rashin fahimta kallo ne na ba kayi mani ba. Da sauri Dr.Aqeel ya janye idanuwansa a dan haryarce yayi hanyar Get din domin fita yana TUFKA DA WARWARA game da Huzaif sosai yake jin hankalinsa bai kwanta dashi ba... "Yah Dr.Aqeel". Kamar daga sama yaji muryarta na fadin haka ko bai ma dauki muryar ba mace daya ce ya sani ta na ambatar sa da wannan sunan a hankali ya lumshe idanunwa yana buɗe su kanta yana ware idanuwansa sosai lokaci guda ya jefa tunanin da yake yi a kwandon shara ya sanyawa fuskarsa murmushi mai karfi hannayensa ya sarke a kirjinsa yana jiran karasowarta fuskarta ita ma da murmushi numfashi taja lokacin da ta iso gareshi. "Daga ina kike Mariya?". Ya fadi yana mai tsare ta da idanu da alamun tuhuma. Gyaɗa kai tayi kafun ta numfasa tayi kasa da kai. "Umma ce take bukatar wannan". Ta fadi tana mai nuna masa bakar ledar dake hannunta dauke da kankana da ayaba. Ware idanu yayi kafun ya gyada kai "Naje dakin ai bakya nan ita kuma ta zaga bandaki ganin ki da banyi a dakin ba shi yasa ma na fito waje". Ware idanu tayi tana murmushi. "Sai kace wacce za a sace shine ka biyo sahu". "Uhmm Mariya kin ga wuce muje ciki nan ai a hanya muke ko". Ya fadi yana mai kafeta da ido ba ta ce da shi komai ba suka fara takawa yana gaba tana biye dashi a baya sosai take kallon yarda yake tafiya cikin kwanciyar hankali da natsuwa lokaci guda ta dubi kanta sai taji wani iri a zuciyarta yanayin shi da ita sun bambanta sosai. Sosai hankalin ta yayi nisa wajan kallon Dr.Aqeel tana tunanin yarda har ya amince ya shigo rayuwarta a yarda take wanda take ganin rashin dacewar haka kamar akwai nakasu a tarayyar sosai... Ba ta kai ga gama lissafin tunanin ta ba kamar ance ta daga kanta wa zata gani da sauri taja da baya tana Ambaton Allah idanuwanta a warwaje wani irin bugu taji kirjinta yayi har sai da ta kai hannunta ta dafe rintse ido take yi gani take kamar a mafarki ba gaske ba sosai tsoro da wani irin yanayi yake bayyana a jikinta sosai take jin wani abu mai girma na saukar mata a zuciyarsa sosai taji zuciyarta ta ta shiga tsalle cikin wani irin yanayi wanda ta rasa a mizanin da za ta ajje shi ba abin da ke mata yawo aka sai sautin marin da tayi masa a can baya gani take kamar yanzu komai ya afku sosai taji ranta na baci da wani irin abu mai girma a hankali ta buɗe idanuwanta tana sauke su akansa sosai ta hango yarda idanuwansa suka kaɗa sukayi jajir sosai take hango wani abu mai kama da tashin hankali cikin idanuwansa gabadaya take ganin yanayinsa a firgice yake sosai take hango yarda ya sauya ba kamar da ba yarda ta ganni sosai ta hango rauni mai girma a tattare dashi ba tare da jarumatar da ta san shi da ita ba "Yaa Allah!". Ta furta cikin karfin hali domin ji take komai yana wargaje mata na tunaninta sosai take jin wani abu na yawata mata cikin gangar jikinta gami da zuciya da ruhi wanda ta kasa gane menene haka din. A hankali ta fara kokarin taks kafafuwanta da take jin sun sunyi mata nauyi sosai ji take kamar dutsen dala aka daura mata numfashi take ja yana kufce mata sosai tayi kokarin jan kafarta har ta iso in yake jingine jikin motarsa tana kokarin gifta shi kamar sautin muryarshi taji ya ambaci sunanta da sauri ta waiga ta sauke masa idanuwanta shima ita yake kallo da wani yanayi wanda ta kasa fassara ko na mene ne abu mai nauyi da girma ta ke hangowa cikin idanuwansa wanda hakan ba karamin narkar mata da jiki yake yi ba gabadaya taji tunanin kwanyarta na wargajewa. Muryar Dr.Aqeel ta jiyo kamar daga sama hakan ya farfado da ita daga sumar da take tsammanin tayi sosai ta dago kanta ta dube in da yake dan nesa da ita tsaye hannayensa cikin aljihun wandonsa wani kallo taga yana yawatawa dashi a kanta wanda hakan ya kara firgitata sosai da sauri tayi kasa da kai kafun ta dago ta dubi Huzaif wanda ya gama zama kalar tausayi wani kallo ta watsa masa wanda ita kanta ba ta san ya akayi tayi masa shi ba. A hankali ta fara takawa kafafuwanta na rawa sosai abu mai girma take jin ya danne mata zuciya yana kara luguiguita mata da gangar jiki da ruhi kanta a kasa ta isa wajan Dr.Aqeel wanda take jin kallon da yake watsa mata kamar ana watsa mata garwashi wuta. "Waye waccan?". Taji muryarsa ta ambata da wani irin yanayi wanda ta tabbata bacin rai ne a cikinta sosai da sosai ba ta san mai zata ce masa ba bata san wata irin amsa ya dace ta ba shi ba sosai ta fuskanci yana cikin yanayin bacin rai wanda ta rasa mai yasa hakan ya bayyana shin ko dai ya san Huzaif ne ko dai ya san wanene shi. Tambayoyin da su dinga mata shawagi kenan cikin kwanya suna kara haifar mata da tashin hankali mai girman gaske. "Dake fa nake Mariya kika yi shiru wanene waccan kin san shi ne?". Sosai taji muryarsa ta kara buɗewa da sautin fushi a cikinta wani kaɗawa taji cikinta yayi ba ta taba zaton akwai ranar da za taji muryarsa haka ba bata taba zaton akwai ranar da zata ji magana irin haka mai dauke da daci a cikin ta ba girgiza kai ta shiga yi a hankali kafun ta kokarta jan numfashi. "Ban san shi ba kawai dai...". "Kawai dai me?". Ya tare ta da sauri har lokacin muryarsa ba ta canza ta koma yarda ta santa ba. Wani karfi taji ya zo mata cikin zuciya da sauri ta dago idanuwanta a rintse ta sauke su saitin Dr.Aqeel kafun ta juya ta kalli inda Huzaif yake tsaye har yanzu tana hango irin tashin hankalin da yake ciki. "Gani nayi kamar yans cikin Matsala sosai naga haka a idanunsa shiyasa na ji ba dadi...". Ba wai don ya yarda da maganar ta bane dari bisa dari domin zuciyarsa taki yarda da abin da yake gani jan numfashi yayi mai tauri yana kokari ajje maganar tata a zuciyarsa yana yarda da cewa ita ta hango tashin hankali game dashi ne shiyasa ta nuna jajantawa gareshi duban Huzaifa yayi daga inda yake tsaye yana hango tashin hankalin da yake ciki idanunsa sosai ya fuskanci wani abu cikin Maganar Mariya kuma zuciyarsa na karyata abin da yake zargi ba tare da yace da ita kala ba ya juya ya cigaba da tafiya jan numfashi tayi ita ma tana sake kallon Huzaif kafun ta kau da kai hadi da hadiye wani abu mai girma da ya tsaya mata a wuya ta daga kafafunta ta bi bayan Dr.Aqeel zuciyar cunkushe da abubuwa ma bambanta wanda ta kasa gane in da suka sanya gaba.. [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA GOMA SHA TAKWAS. *In ka rike mani za na rike maka ribar zama yarda da juna farin cikina zana sanar maka kai ka damu dani.* --Usaini Danko A hankali yake ajje komai na shi kan table din dake girke cikin kayataccen office din sa kallo daya zakayi masa ka gane hanzarin da yake yi cikin aikinsa gabadaya hankalin sa bai wajan abin da yake yi idanuwansa na wajan kofar office din ji yake yi ajikinsa akwai wanda zai shigo zuciyarsa tana sanar dashi hakan. Bayan ya kammala komai a hankali ya fara takawa kan ƙafafuwansa don ji yake yi kamar abin da yake muradin gani kum zuciyarsa na sanar dashi tabbatarsa kamar ba zai tabbata ba gareshi sosai yake ganin tafiyar lokaci wanda yake hango kurewa a cikin sa duk dakika daya gani yake yi kamar tafiyar awa daya ce. Wajan sakatariyarsa ya dosa yana faman jan numfashi. "Sir Morning". Abin da ta fadi kenan bayan ta dago kanta jin alamun mutum kusa da ita. Hannu ya daga mata alamun amsawa kafun ya shiga waige-waige na yan dakiku sannan ya sauke idanuwansa akanta yana mai nisawa. "Areefa ta shigo aiki yau kuwa?". Mamaki taf! A fuskarsa take dubansa sosai take lura da canjin ogan nata tunda Areefa ta shigo cikin ma'aikatar nan gaɓadaya hankalinda da natsuwarsa suka karkata akanta ba ta san mai hakan ke nufi ba...ko da dai bai kamata tayi mamaki domin ta san waye Dr.Erena tuni ta diga masa ayar tambaya katotuwa. Kaɗa idanu tayi kafun ta motsa tika-tikan laɓɓanta wanda suka sha jan jambaki sai faman kyalli suke yi. "gaskiya bana zaton ta shigo don ban ji duriyar ta ba yau sam". Ta karashe tana mai kafeshi da idanuwa sosai ta sosai kai taga ya shiga girgizawa yaka faman cizon laɓɓansa gami da haɗa hannayensa waje daya yana lankwasawa suna bada wani sauti mai zurfi. A hankali ya fara taka kafafuwansa da sanyi a cikin su amma yarda yake tafiyar cikin hanzari bai bayyanar da haka din ba kofar fita daga sashi ya dosa yana faman hanzari cikin tafiyarsa cikin kankanin lokaci ya sauka daga benen zuwa tsakiyar cikin company din idanuwansa ya ware yana yawatawa cikin sashi da sashi na ko ina. Ya jima cikin wannan yanayin kafun ya isa wajan daya daga cikin ma'aikatan da suke nan din ko wanne da bangaren sa kamar office. "Mufeeda Please ko kin ga Areefa ta shigo yanzu?". ya fadi har lokacin idanuwansa ba su tsaya waje daya ba. Dago kanta tayi jikinta sanye da abaya kamar ko yaushe dubansa tayi da wani irin yanayi kafun ta kau da kanta sosai taji sunan da ya ambata ya shiga kuwwa cikin kwakwalwarta sosai take jin sunan yana haifar mata da wani irin yanayi mai girma gareta zuciyarta taji tana zaro mata wani labari mai girma da ta daɗe da binne shi a filin zuciyar ta ta sunan Areefa take ji kamar a mafarki abubuwa da yawa take ji a ranta game da sunan. Nisawa tayi cikin wani irin yanayi mai girma kafun ta dago kanta ta sauke ga Dr.Erena wanda shi a wannan lokacin sam! hankalinsa baya kanta sai faman watsa idanuwansa yake yi cikin ko wani sashi na ma'aikatar har izuwa babbar kofar. "Areefa". Kamar daga sama taji bakinta na nanata sunan da wata irin murya mai zurfi da wasu abubuwa masu girman gaske. "Ban san taba ban ma taba ganin ta ba!". Muryarta da zurfi a cikinta tashiga fadin haka da alamun bacin rai tattare da ita musamman yanayin da fuskarta ta sauya lokaci guda bacin rai sosai ya samu masauki a ko wani sashi na filin zuciyarta da ruhinta. sosai yaji sautin muryar Mufeeda akansa wanda tunda suke da ita bai taba jin tayi magana mai zafi haka ba sosai yake kallon ta cikin yanayi na mamaki kafun ya nisa. "bakuwar da ta zo last week fa nake magana wacce kuke matsayi daya da ita". Sosai yake yawatawa da idanunsa akanta yana kallon yarda komai nata ya sauya lokaci guda kai ya shiga gyaɗawa kafun ya juya ya doshi babban kofar da zata sadaka da reception din Company din. Tsaye yayi hannayensa zube cikin aljihun bakar suit dinsa sai faman yawata idanuwansa yake yi ta in da zai hango can wajan Parking ya tsayar da ganinsa yana bin motocin wajan da idanunsa daya bayan daya bai dire a ko ina sai kan wata bakar marsandi wacce kallo daya zakayi mata ka gane sabuwa ce fil. Ajiyar zuciya ya ajje hakan ya tabbatar masa da Areefa na cikin Company din nan amma kuma ya akayi bai ganta ba har sashinta ya duba nan ma bai ganta ba ya tambayi abokan aikin ta suma sunce ba su ganta ba mai hakan ke nufi?. A hankali ya fara juyawa kan kafafuwansa domin koma cikin Company zuciyarsa cike da tunnain Areefa da dalilin da yasa bai ganta ba cikin Company kuma alamun ya nuna ta na ciki tunda ga motarta nan hakan ya tabbatar masa da zuwan ta da wannan tunanin ya koma ciki bai sake duban kowa ya hau matattakalar da za ta haura dashi zuwa sashin sa. Mufeeda dake zaune tun dazu ta zabga tagumi tun da ya zo ya sanar da ita wacce yake nema ya fada mata sunan da yake cigiya shikenan taji ta komai nata ya canza sosai taji wani iri a jikinta har ma da zuciyarta sosai take jin wani abu mai nauyi mai dauke da bacin rai ya samu masauki a zuciyarta a hankali take ajje numfashi tana duban Dr.Erena zuciyarta na kara tabbatar mata da abin da take zargi. Gyaɗa kai takeyi tana yatsine fuska gami da tura laɓɓanta cikin bakin sai da ta dauki lokaci mai tsayi a haka kafun ta ajje komai gefe ta cigaba da aikinta amma ta zuciyarta sai kawo mata abubuwa take yi wanda yake kokari addabatar ya hana ta aikinta. Tana cikin kokawa da zuciyarta kamar daga sama taji sautin takalmi ya karaɗe cikin wajan gabanta ne ya buga ko ba a fadi mata ba tabbas ta gane ko wacece mai wannan tafiyar bata dago kanta ba sai dai aikin da take yi cikin Computer ta tsayar dashi cak! hannayenta ta janye daga madannan computer din ta hade su waje guda tana sarke su a hankali kafun ta dago kanta a daidai lokacin ita kuma ta karaso daidai wajan da take hannunta rike da jaka mai kalar Gold da wasu yan duwatse masu kyalli da akayi mata ado da su jikinta kananun kaya ne wando da riga sai abayar da ta daura a kai gaban rigar abuɗe yake ta yane kanta da gyalen abayar fuskar nan ta sha Make-up sosai hanyarta a kunnan ta sai faman sakin murmushi take yi da alamun wayar da take yi din tana jefa cikin nishaɗi. Kuri Mufeeda tayi mata da ido tana saka dan guntun biron dake hannunta cikin bakinta rana jujjuyashi tana yawatawa da idanunta sosai akan Areefa da ta tsaya daidai saitinta bugun zuciyarra na karuwa sosai da sosai abin da take zargi ne take ganin tabbatarsa zuciyarsa na kara hasko mata abubuwa da dama da suke kara tabbatar mata da zarginta. Yaa Allah!. Abin da ta fadi kenan lokaci guda tana dafe kanta da taji yana sarawa runtse idanuwanta tayi sai sai da ta dauki sakann kafun ta buɗe su har zuwa lokacinAreefa na nan tsaye sai dai ta gama wayar ta sauke duban Mufeeda tayi wacce ita idanuwanta na kanta lokaci guda sua sarke a idanuwansu sosai suke kallon junansu wasu abubuwa ne masu girma suke wanzu a zuciyoyinsu sun dauki mintoci a haka kafun Mufeeda ta kau da idanuwanta gami da yin kasa da kai ita kuwa Areefa kafadun ta daga gami da nuna halin-ko-in-kula ta ƙyaɓe baki tana mai daga wa Mufeesa hannu ta raba ta ta wuce cikin takunta na musamman da duk lokacin da zata shigo cikin Company din take yin sa. ******* Sosai hawaye ke kwaranyo zuwa saman fuskarta sosai take jin zuciyarta na zafi da raɗaɗi sosai take jin tashin hankali wanda ba ta tsammanin ba mai girma baɓe a rayuwarta ba ta san ya zata koyi rayuwa ba a yanzu bata san ya zata koyi rayuwa ba batare da wadannan dangin ran ba bata san ya zuciyarta zata koyi kewarsu ba sosai take jin abu mai girma na samun waje afilin zuciyarta yana zama duk jikin ta take jin yayi sanyi yana haifar mata da abubuwa masu girma da kara dagula mata lissafi ba ta san ya rayuwa zata kasance mata ba nan gaba ba ta san wata irin rayuwa zata buɗe ba a shafin duniyarta in ta bar wannan wajan. Hannunta ta sa ta shafe hawayen da suke sake balle mata wasu na bin wasu hada kayan su take yi cikin yanayi wanda ita kan ta ba ta san ya zata fassara shi ra san dai akwai tashin hankali mai girma da zai zo mata ko ma tae ya zo mata ba ta san ya zata dauke shi ba ta san ya za ta ajje tashin hankalin nan a zuciyarta za ta bar su za tayi kewarsu ta tabbata dole ne su rabu rabuwa ta har abada wanda bata tsammanin za su sake hadu a duniyar nan domin da ma can matsayin su ba daya bane ta sani sam ba su dace da zama a inuwa daya ba har su shaku ta sani zuciyarta...zuciyarta ba tayi mata adalci ba ba ta yi mata daidai ba ta sani tayi sake sosai da ta bar zuciyarta ta shaku da mutanan da ta san tabbas su rabu ko tana so ko bata so domin duniyarsu ba daya bane suna da tazara mai girma a tsakaninsu akwai katanga mai girma da tayi musu SHAMAKI a tsakani yau ta ga ILLAR SABO a rayuwarta tabbas sabo shi ake yi wa kuka dole tayi jinyar zuciyarta wanda ba ta san ranar da zata warke ba daga ciwon da ya kamata mai girma wanda laifinta ne da tayi sake har ta bar zuciyarta da gangar jikinta sukayi saboda da wadannan mutanan masu ALHERI da YAƘANA. "Mariya!". Taji muryar Umma na ambaton ta cikin yanayi mai cike da rauni da kuma rarrashi. Da sauri ta sanya hannunta ta shafe hawayen da suke saukar mata kafun ta kokarta janyo yaƙe muryarta na rawa ta ansa mata gami da juyowa ta na fuskantar ta kallon ta take da duk wani rauninta dake cikin zuciyarta tana jin yarsa ruhinta da gangar jikinta suke haifar mata da wani irin yanayi mai wuyar fassaruwa sosai take kallon Ummanta da yanayin da take ciki ta rame sosai sai dai kallo daya zaka yi mata kasan tana samun kulawa komai nata yayi normal duk wani abu dake damunta ya kau yanzu lafiya kalau take tana iya magana sosai cikin hankalinta ba tare da an samu matsala ba ko ya ya take sosai tayi wa Allah godiya da wannan ni'imar da yayi musu sosai take sake gode masa tafi kowa farinciki da wannan lamarin tafi kowa farin ciki da samun lafiyar Ummanta sosai take jin zuciyar na rage duk wani nauyi mai girma abu daya yake kara dakula mata lissafi in ta tuna shi Mahaifinta sosai take shiga tashin hankali mai girma sosai komai nata ke kara hargitsewa in ta tuna rashin matsaya da take dashi akam mahaifinta kullum cikin tunaninsa take ba ta san mai yasa ya tafi ya bar su ba a daidai lokacin da suke bukatarsa a filin duniyarsu ba ta san mai yasa ya bar su tsayin wannan lokacin ba bata san mai yasa ya dauki kafarsa ya bar su ba batare da ya sanar da su in da ya dosa ba sosai take shiga tashin hankali mai girma in ta tuna wannan lamarin. Nisawa tayi kafun ta amsa kiran da Umman nata tayi mata. "Ban san mai kike nufi da wannan kukan ba Mariya, Ban san mai kike so kuma ki daukowa kan ki ba, na lura sosai kike jin dadin zubda hawayenki baki san hakan yana matukar sanya ni cikin damuwa ba". Shafe hawaye tayi sosai take jin maganganun Umma a zuciyarta sosai take fuskarta gaskiyar abin da Umma ta fadi sai dai bata san ya za tayi da abin da yake a zuciyarta ba sosai take jin rashin dadi ba ta san ya za tayi ta hana idanunta zubda hawaye ba. "Umma Kiyi hakuri ban san ya zan yi in hana su zuba ba ne sosai take jin kewa a raina sosai nake jin rashin jin dadi a ko ina nawa saboda su mun shaku Umma suna da alheri sosai a duniyar su ban san yaushe za mu sake haduwa ba in muka rabu...". Zuciyarta tayi rauni sosai muryarta ta karye hakan ya sanya ta yin shiru tana mai toshe bakin ta da taji kuka na shirin kufce mata. "Yaushe zaki girma Mariya mai yasa kike abu kamar wata yarinyar da ke goye wa ya gaya miki kun rabu kenan har abada shin ce miki akayi daga nan lahira zaki tafi ba a duniyar zaki zauna ba to bari kiji mutum da mutum suna rabu sai su shafe shekaru masu yawa har su fiddo tsammanin sake hadƴwa amma cikin iko na Rabbi sai ki ga sun hadu har sun sake wata rayuwar a filin duniyarsu don haka ki daina YANKE TSAMMANI akan abin da bakin san yarda zai kasance ba Allah kawai za ki saka a lamarin ki ba fa rabu rigima a kayi ba balle ki ce tsakanin juna ba za a so sake haduwa ba ALHERI ne ya hada ku kuma kin san shi alheri a ko ina yake ba ya tafiya a banza". Ba wai tana maganar nan ba ne don ta yarda ita akaran kan ta a,a kawai dai so take yi ta kwantarwa 'yar ta ta da hankali domin yanayin da taga ta dau lamarin mai gira a zuciyarta ko da yake tana da gaskiya zama lafiya aka ce yafi zama dan sarki zaman da akayi cikin aminci da mutunta juna dole a ji ba dadi wajan rabuwa ko zama da mutum kayi kullum kuna fada dole in za ku rabu kaji rashin dadi a ranka ta dani ita a akaran kanta abin da Mariya tayi ba ta ga laifin ta ba domin ta lura akwai sabo da shakuwa sosai a tsakaninta da likitocin asibitin tana kallon yarda suke mutunta ta da ahalin ta tana kallon yarda 'yar ta ta take ganin girman su da ba tare da raini ko wani abun kiba fiye da KWANA SITTI da tayi a asibitin nan kamar yarda taji likitan na fadi ta san dole ne su shaku sosai shakuwar da ba za su so rabuwa ba amma ba yarda za suyi rayuwa ta gaji haka aka rabu da mutum ma zuwa lahira kuma aka hakuri balle wannan a na cikin duniyar sai dai ace ba waje daya ake zaune ba. Gyaɗa kai tayi cikin yanayi na tausayawa shiru ne mai dan tsayi ya ratsa cikin dakin ba abin da kake ji sai ajjiyar numfashin Mariya lokaci lokaci tana jan hanci da alamun kuka a ciki kawai daurewa take yi ba ta taba zaton za su rabu ba ba ta taba zaton magaɓar rabuwarsu a wata rana ba za ta tabbata kamar yarda Dr.Karami ke fada mata ashe da gaskiyar wannan ranar za ta zo filin duniyar su kowa ya kama gabansa ashe duk maganganun da yake mata masu shige da WASIYYA gaskiya ne amma ta kasa sanya hakan a zuciyarta taki yarda ta maganar tsa da take kallo a matsayin kanzon kurege bata san ruɗi da ya dauke ta ba bata san abin da ya shigar mata kai da zuciya ba ya hana ta hadda ce karatun Dr.Karami yanzu ga ranar ta zo ga cikin ta tsamo tsamo amma ta kasa yin komai sai nauyin zuciya da tashin hankalin da ta ke hangowa... Sallamar da ta amsa kuwwa cikin dakin ne ta dakatar da ita daga zancen zuccin da take sosai taji wani irin bugun zuciyarta ya canza salo sosai taji wasu katangun tashin hankali suna kokarin rikito mata akai wani kuka mai karfi taji yana kokarin kufce mata bakin ta na rawa ta shigo kokarin amsa musu amma hakan ya gagara da gudu tayi hanyar Toilet din dakin hannayenta rufe da bakin ta kuka sosai take jin yana taho mata ta na shiga ta mai da kofar ta rufe durkushewa tayi a tsakiyar Tiolet gami da sakin wani irin kuka mara sauti mai matukar taba zuciya da ruhi da duk wani mai jinsa. Sosai Dr.Karami yaji gabanda ya buga yanayin da ya ga Mariya a ciki idanuwansa ya sauke kan Umma da tayi kasa da kai sosai take jin wani iri a zuciyarta raunin da ta gani game da 'yarta ya haifa mata da tausayi mai girma a zuciya ta sani 'yarta ta shaku da su sosai shakuwar da sai anyi dagaske kafun a rabu dole zuciyoyi su shiga halin damuwa dole gangar jiki su shiga hali na rashin jin dadi sosai da sosai. Kallon kallo suka shiga yi tsakanin su Dr.Karami da Dr.Aqeel sosai suke jin wani iri a zuciyoyin su musamman Dr.Karami don ji yakeyi kamar ya falla da gudu ya bita ya rarrashe don ya san tabbas ba abin da yake damun ta sai maganar rabuwarsu ba tun yau ba ya lura sosai take nuna dauwa da tsoro duk ranar da ya yi mata maganar rabuwar su bai san abin zai yi tsanani haka ba ko d yake shi tashi zuciyar yanzu haka ciwo mai girma yake jin yana fama dashi jarumta ce kawai take hana shi bayyanar sirrin dake ransasosai yake kewar Mariya duk da dai a ransa ba ya tunanin rabuwa za suyi ba ya hangowa rabu sam-sam cikin wannan lamarin amma dai yau a wannan rana shi a karan kan sa yana jin ba dadi don ji yake yi kamar wanda ya tashi daga cuta saboda rashin kwarin jiki. Duban Dr.Aqeel yayi wanda shi dai yanayin ya nuna akwai abin dake damun sa a ransa sosai da sosai fuskarsa ta nuna rashin walwala jikinsa yayi sanyi sosai idanuwansa sun kada kadan kamar mai son fashewa da kuka. Ba tare da yayi masa magana ya doshi kofar Toilet yana kwankwasawa a hankali yana kiran sunanta sosai yake jiyo shasshekar kukanta wanda haka ba karamin taba masa zuciya yayi ba sosai yake jin tausayi da wani abu mai matukar girma suna wanzu a filin zuciyarsa a hankali ya cigaba da kwankwasa amma ko alamun za ta yi magana juyowa yayi ya kalle su suma shi suke kallo musamman Umma wanda ta gama karantar yanayin su su duka sosai take jin tausayinsu duk su ukun na samun waje a zuciyarta ji take ina ma tana da wata dama da zatayi amfani da ita domin fidda su cikin wannan yanayi amma ina! ta san ba ta dashi gyaɗa kai tayi tana kau da kai daga barin kallon Dr.Karami. A hankali ya rike Handle kofar ya turo sai ya ganta abude take da sauri ya karasa turawa yana mai sanya ƙafafuwansa da yake ji kamar za su zubda shi kasa saboda raunin da ya ji sunyi sosai. Durkushe ya hango ta hade jikinta waje daya sai faman jan numfashi take yi mai zafi sosai zuciyarta take jin tana wani irin harbawa kamar zata faso kirjin ta ta fito waje komai take ji yana kwance mata komai na cikin duniyar take ji yana sauya mata lokaci guda. "Mariyaaa!". Ya fadi muryarsa da wani irin rauni mai girma idanunwansa a kan ta a hankali ta shiga kokarin dago idanunta da suka kaɗa sosai sukayi jajir kamar wanda aka watsawa barkono wani irin bugu zuciyarsa tayi wanda hakan sai da ya sanya shi sanya hannu ya dafe kansa duniyar yaji tana juya masa lokaci guda kau da kansa yayi don ba zai iya kallon idanuwanta a yarda suke ba wasu abubuwa ne masu girma yake ji game da kallonta suna faru dashi a filin zuciyarsa. "Ban san mai ya kike haka ba, ban san mai kike wahalar da kan ki haka ba, Haba mana Mariya mai yasa kike zurfafa lamarin nan haka rabuwarmu ai ba ta na nufin mun rabu har abada bane a,a muna nan tare a duniya daya har zuwa numfashinmu na karshe." Ba ta san ya zata dauki maganar ta sa ba bata san ya zata daura su a MIZANIN HANKALI ba sosai take jin zuciyarta taki aminta da zancen sa sosai take jin kawai fadi yake yi domin ganin ta daina kuka rintse idanunta tayi kafun ta mike kan kafafuwanta cikin wani irin yanayi mai rauni. "Ta ya ya kake so na anshi maganar ka ta ya ya ka ke so na gasgata abin da kake cewa bayan nasan dole mu rabu dole mu raba duniya bana zaton maganganunka za suyi tasira Yah Dr.Karami kawai ka fito fili kace mani yau ce rana ta karshe a duniyarmu da muka hadu yau ce rana ta karshe a garemu yau ne za mu rabu da juna...". Wani irin nishi tayi kafun ta gyaɗa kai hawaye su zubo mata wanda Dr.Karami yake jin su kamar saukar ruwan zafi a jikinsa. "Ban san ko zaka yi maki alkawaro ba sosai na yi sabo da kai a duniya ta ban sani ba ko za kayi mani adalci a duniyarka ka kasance dani mu ke mutunci ba zan taba mance alherin ka ba kai da sauran Al'umma sosai nake hango matsayin ka a matsayin dan uwa na jini ban da yan uwa so nake ka zama dan uwa gareni ka kasan ce mani dan uwa bayan Mu'azzam don Allah in kayi mani haka zan yarda kuma zan rike duk abin da kace mani in har ka rike mani abin da nace da kai". Rintse idanu yayi sosai zuciyarsa da kwakwalwarsa yake jin suna wani shawagi dashi a wani mataki wanda bai taba jin kan sa a ciin sa bai san mai zai ce mata ba bai san wani kalamai zai yi amfani da su wajan yi mata magana ba abu daya ya sani shine ba zai iya rabuwa da ita ba zai so ace yarda take maganar nan shim ya fadi mata shima haka yake ji ransa kamar yarda take ji. Nisawa yayi kafun ya kokarta dubanta yana sani murmushi mai karfin gaske. "Na yarda tuni na yarjewa zuciya ta zan ci gaba da zama dake a duniyata har zuwa karshen numfshi ne na yarda na aminci da maganarki na rike miki alkawari ke ma ki rike mani kamar yardakika fadi". Shafe hawayenta tayi kafun ta saki wani murmushi kamar yarda ta ga yanayi mata. Alamu yayi mata da kai su fice daga Toilet din tana yatsine fuska alamun kyankyami kunya taji kai a kasa ta bi bayan sa zuciyarta na rake duk wani nauyi da ya tokare mata kirji tun lokacin da aka sanar da su sallamar su da akayi. Bin su sukayi da kallo Umma ta dubi Mariya tana harararta kasa tayi da kai kafun ta dubi Dr.Aqeel wani kallo taga yana yi mata wanda sai da ya sanya gabanta bugawa da sauri tayi kasa da kai tana cizon laɓɓanta abubuwa da yawa suna rikita mata kwakwalwa a tsakanin Dr.Aqeel da Dr.Karami abubuwa da yawa take hangowa a tsakanin su wanda ta kasa gane menene iya tsayin tunaninta da tsayin lokacin da ta diba tana nazarin su ta kasa gane mai suke nufi da wasu abubuwa da ta lura suna yi mata.... [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA GOMA SHA TARA. "Innalillahi wa inna ilaihir raji'una mai nake shirin gani ni marka? Hafsi! Hafsi!! Hafsi!!!." Goggo Marka dake zaune bakin kofa tana kadin zarenta ta mike tana tafa hannaye tana fadin haka idanuwa warwaje lokacin da ta ji sallamar su Mariya jikin ta har ɓari yake yi ta shiga dubansu kamar wanda ta ga wani mugun abu. Cak! Suka tsaya suma suna dubanta musamman Mariya da idanuwanta su kayo waje tana duban ta ganin yanayin da ta nuna juyawa tayi ta dubi Umma kafun ta sake mai da kallonta zuwa wajan Goggo Marka. "Mariya Habeeba daga ina kuma haka?". Ta fadi cikin yanayi na mamakin ganin su. Suma mamaki ne ya cika musu zuciya sosai da sosai sun rasa abin yi gabakidayan su sai bin ta da kallo kawai suke yi suna faman gyaɗa kai a hankali Mariya ta ja jiki a sanyaye ta isa bakin kofar dakin su da yayi kaca-kaca kamar wani kudundubi kofar dakin su har an girgiɗe ta labulan kuwa an yi fata-fata dashi ta na hango tsakar dakin yarda ya zama kamar wajan wasan yara sosai taji ranta ya sosu matuka gaya tsaki ta ja kadan kafun ta ajje kayan da suke hannunta wani irin duba tayi wa Goggo Marka da tayi tsaye fuska cike da mamaki sosai Hafsi da ta fito da daurin kirji kai ba dan kwali gashin kan nan nata yayi wani kerere kamar dambun karangiya sai fama yawatawa da idanunta take tsakanin Umma da Mariya cikin yanayi na mamaki kallo daya zakayi mata ka gane a firgice ta fito daga cikin dakin barci ne a idonta. Kau da kai Mariya tayi kafun ta isa in da Umma tayi tsaye kamar wacce aka dasa kallo daya zakayi wa fuskarta ka gane bacin ran dake kunshe a zuciyarta ansar Mu'azzam tayi ta goya sannan ta dubi Umma tana mai rike mata hannu suka baro wajan suka iso kofar dakin nan bari ta samu damar dan gyara wajan sannan ta dauko zani cikin kayansu ta shimfiɗa wa Umma ta zaunar da ita daga nan ta shiga dakin tsaye tayi tana bin sa da kallo wani haushi da takaici gami da tukukin bakin ciki suka cika mata zuciya sosai take ganin yarda dakin ya sauya gabadaya kamar dakin mahaukata kallo take tana tunanin ta ina ma zata fara gyaransa don ta san tabbas wannan dakin ba zaunuwa zai yi ba haka kwafa tayi sannan ta fito daga cikin dakin Umma ta duba cikin yanayi na damuwa. "Bari na siyo tsintsiya Umma domin wannan dakin ba zaunuwa zai yi ba dole a gyara shi". Gyada mata kai kawai tayi itama ba tare da ta sake cewa komai ba ta duba cikin kayan su gudan duba ta dauko cikin kudin da Dr.Aqeel ya bata ta fice daga cikin gidan bisa mamaki har yanzu suna nan ba su tafi ba baki ta saki tana duban su kafun ta taka ta isa wajan su. "Uhmm wai har yanzu...". sai kuma tayi shiru ba tare da ta karasa abin da tayi niyyar cewa ba ganin irin kallon da Dr.Karami yake yi mata na alamun tuhuma. "ina zaki je kuma da wannan ranar daga dawowarku?". Shiru tayi kamar ba za tayi magana ba can ta nisa. "tsintsiya zan sayo dakin zan share yayi kura ne sosai da sosai ba zai zaunu ba". ta karashe tana mai yatsine fuska kamar za tayi kuka sosai take jin wani iri a ranta ba ta so ta fito ta tadda su ba ba ta so a wanna lokacin ta sake saka su a idanuwanta ba ta so ace yarda ta baiwa zuciyarta hakurin kewarsu na dan lokacin nan suma sun yi hakan sun tafi ba za ta so wani sabon lamari ya sake afkuwa ba a nan wajan domin ba zata manta tsawon lokacin da suka shafe a nan wajan ba tun isowarsu ake abu daya sai da Umma tayi da gaske sannan suka shiga cikin gidan bayan sun yi sallama amma kuma abin mamaki ta fito ta tadda su. "Bari naje na sayo Umma na jira na". Ta fadi cikin yanayi na damuwa domin ba za iya tsayuwa tana kallon su ba sosai take jin zuciyarta na zafi da raɗaɗi ba ta jira cewarsu ba ta fara tafiya cikin yanayi na sanyi jiki sosai ko da ta isa shagon mai tazara kadan da gidan su makalewa tayi taki dawowa tana hango su ba ta ga alamun suna da niyya tafiya ba sam! ita kuma ba ta so su sake gamuwa a cikin halin da take ciki a yanzu so take ta bai wa zuciyarta hakuri so take ta fara koyon zaman kadaici tun yanzu don ta san tabbas dole wata rana su dau lokaci mai tsayi kafun su hadu kuma ya zame mata tilas ta yi abin da Ummanta ba za ta shiga damuwa ba dole ta kau duk wata damuwa a zuciyarta don ganin walwala ga Ummanta. Numfashi taja kafun ta hango sun shiga motarsu ta lura sosai kamar sun damu da rashin dawowarta kuma ta san saboda su taki dawowa don haka suka yanke hukunci tafiya hakan yayi mata dadi sosai da sosai sai da taga sun fice daga layin su sannan ta tako cikin sarsarfa domin a tunanin ta kila su dawo. ***** "Mun shiga uku". Cewar Hafsi tana daura hannu akai idanuwa warwaje kafun ta sake jan numfashi mai dauke da tashin hankali. "ki ka ce mani sun tafi kenan har abada ba za su dawo ba, amma kuma ga su sun dawo kuma kin ce mani Habeeba ta zama MAHAUKACIYA amma dube ta kalau ba alamun hauka a tare da ita". Goggo Marka da ta yi zaman yan bori kofar daki ta zabga tagumi tana duban Habeeba da ɗan dake hannunta wasu katangun tashin hankali taji suna rigizo mata akai ji take yi duniyar na juya mata ba ta yi zaton haka zata faru ba bata taba kawo hakan akan ta ba ta yi zaton sun tafi kenan ko duriyar su ba za a sake ji ba a duniyar nan tuni ta saki jiki take shan sharafin ta ganin lokaci sai tafiya yake yi kuma ba su dawo ba hakan ya kara gasgata mata zatonta amma yau rana tsaka irin wanna mugun abu ya zo mata wani numfashi taja ta fesar kafun ta dubi Hafsi murya kasa-kasa domin bata so Habeeba ta ji maganganun da suke yi. "tuni fa aka tabbatar mani da ta haukace ita da 'yar ta ta da mijin nata...". Da sauri Hafsi ta katse ta. "Injiwa ya fada miki to wallahi duk wanda ya fada miki hakan karya ne ki dube su fa su duka kalau suke ba abin da ke damun su". Nisawa tayi ta kai hannunta ta na susar kanta. "ina ganin mugun abu kenan da gaske Habeeba ba hauka tay...". Sallamar da Mariya tayi ne ya katse musu hirar da suke yi sukayi wuri-wuri da ido alamun rashin gaskiya kallo daya tayi musu ta kau da kanta a jikinta take ji akwai maganar da suke yi wanda ya dangance su kunuwanta sun jiyo mata kalmar hauka da Goggo Marka take fadi a zancen hakan ya tabbatar mata da Ummanta suke yi wato hauka tayi kenan daukar ta suke a matsayin mahaukaciya wani kunci taji ya tokare mata kirji sosai taji ranta na ɓaci amma sai ta share su ta baiwa banza ajiyarsu ta isa in da Umma kenan zaune ta zabga tagumi da alamun ita ma ta ji hira da suke yi a kanta don idanunta har sun tara kwalla kadan. Sauko da Mu'azzam tayi barci ya ke yi hankali kwance a haka ta mikawa Umma shi ba tare da tace da ita kala ba ta dauki tsintsiyar da ta sayo ta shiga dakin a hankali ta fara tattara kayan su waje daya ta na fitowa da su waje zuciyarta na kunci da bakin ciki sosai take jin tausayin kan su sosai take hango irin kalar zaman da za suyi a gidan nan duba da tayi da halin Goggo Marka yana nan yarda yake ba sauyawa tayi ba sai abin da ya ci uban na da sosai take ganin za su fuskanci yanayin rayuwa a gidan musamman yanzu da suka kasance su kadai ba mahaifinta wanda shi kadai suke samun sauki a wajan sa to yanzu baya nan Allah kadai yasan halin da za su shiga cikin wannan halin ta hau tsaftace dakin yayi kura sosai bayan ta kwashe komi ta samo ruwa ta yayyafa a dakin saboda ba simitin in tana sharewa kuma kura na tashi sosai a haka cikin jarumta ta kammala sharewa sannan ta fito ta barshi ya sha iska kayan su ta ajje su gefe domin sun yi datti sosai suna bukatar zama na musamman domin wanke su sai da ta zauna ta huta sannan ta sake fita ta sayo kayan wanki sabulu da omo ta zo ta ja ruwa sosai ta jika kayan duk abin da take yi akan idon Goggo Marka da Hafsi sai faman bin ta da kallo suke suna faman yatsine fuska kamar sun ga abin kyankyami.. ********* Satin su Mariya biyu da dawo gida izuwa lokacin mutanan unguwa da yawa sun san sun dawo ana ta zuwa musu barka da arzuki da kuma ya mai jiki a nan suke samun labari wajan mutanan gari wai ai Habeeba hauka cewa tayi ta shiga duniya tun da ta haihu cutar hauka ta same ta ba a san in da take ba Mariya da babanta kuma suma sun ba zama duniya ne neman ta tun da suka tafi ba labarin su. Abin yayi matukar daurewa Umma da Mariya kai sosai suka ji a ransu bisa wannan mugun fata da akayi musu na halaka ko daya ke ba suyi mamaki ba tun da sun san halin wacce ta kulla musu wannan makircin kadan daga aikin ta. Ba su ce da ita komai ba sai dai suka barta da Allah domin kuwa halinta yafi karfin su. Kamar ko yaushe yau ma Mariya na goye da Mu'azzam tana dauraye musu kayansu domin tun da suka dawo ko tsinke ba ta bari Umma ta dauke komai ba ita take yi rainon Mu'azzam duk yana wajan ta tun da ba nono yake sha ba sai madara anyi anyi amma ina yaki kamawa ko ya kama ya fara sha sai ya saki dole ta kasance madara ake bashi. "Mariya". Ta jiyo muryar Umma ta na kiranta da sauri ta ajje wanki tana amsawa ta doshi dakin. "Yawwa yar Albarka amshi nan maza ki je gidan kultum ki sayo mani tafarnuwa". Da mamaki Mariya ta dubeta. "Umma Tafarnuwa kuma, me zakiyi da ita?". "Yaa Allah! Mariya kenan. ba fa wani abu bane zan yi da ita kawai kafafuwa na ne naji suna rikewa na san kuma sanyi ne ba wani abu ba shine fa zan yi amfani da ita". dan tsuke fuska tayi alamun rashin son abin da Umma tace. "kawai ki bari Yah Dr.Karami ya zo sai a fada masa ƙafarki na ciwo nasan zai baki magani ni kam ban yarda ki yi amfani da tafarnuwar nan ba tun da ba likita bane yace ki yi amfani da ita". Murmushi tayi ta san halin Mariya sarai tun da ta warke a cutar nan in dai za tayi abu to tabbas sai taji daga bakin Dr.Karami tun da yana zuwa musu lokaci lokaci ya duba jikin Umma. "Shikenan naji taimaka dai ki sayo mani na ajje in ya zo duk abin da ya ce dashi zan yi amfani". Fuskar a dan tsuke ta amshi kudin ta ficewarta Umma na bin ta da ido murmushi a fuskarta sosai take jin kaunar 'yar ta ta a ranta sosai yanayin rayuwarta take burgeta da komai na ta godiya take yi wa Allah da ya bata 'ya kamilalliya mai natsuwa da sanin ya kamata duk da karancin shekarun ta hakan bai hana ta sanin ya kamata ba idanuwanta lokaci guda suka kawo kwalla. "Ina ka shiga ne ina son ganin ka a duniyata ya Allah duk in da wannan bawan naka yake Allah ka tsareshi ka tsare masa rayuwarsa ya Allah ka karkato masa da hankali ya dawo gaban iyalansa suna matukar buƙatarsa". A bayyane take zancen zuciyarta take ji tana yi mata zafi tun lokacin da ta tsinci labarin tafiyar mijinta shikenan komai ya kara jagule mata ta rasa ina zata sa kanta abubuwa da yawa sun rikita mata rayuwa ita ba dangi ba ita ba iyaye ba sannan gashi yanzu miji ba ta san a halin da yake ba sosai take godewa Allah da irin ƙaddarar da ta samun kan ta a ciki sosai take goɗewa Allah da irin jarabtar da ya jeho mata cikin rayuwarta. Dauke hawayen ta sake yi tana mai gyaɗa kai ita kadai ta san abin da take ji a zuciyar ta da kasan ruhin ta sosai rayuwar duniyar nan ke tsorata ta sosai take tsorota da komai na duniyar nan baki dayan sa. ******* Sosai zuciyarta ta buga lokacin da idanuwanta suka hango mata shi zaune saman motarsa ya tallaɓe haba kamar wanda aka aikowa da mutuwa cikin dangin sa runtse idanuwa tayi gani take kamar a mafarki ba gaske ba laɓɓanta ta tura cikin baki tana cizawa a hankali zafin da take ji yana ratsa ta ya tabbatar mata da gaske shi din ne ba wani ba. Kallon sa take da duk wani yanayi da ta tsinci kanta sosai ta hango sauyin yanayi game dashi sosai ta hango canji a gareshi ba kamar kwanakin baya ba wani abu taji yana mata yawo a zuciya sosai take jin jikinta na sakin wani irin yanayi yana kaiwa ga kafafuwanta kamar ba za su dauki gangar jikin ta ba. "Yaa Rabbi!". Ta fadi tana mai kau da kanta tana gargaɗin zuciyarta da ta daina abin da take yi akan Huzaif... "Mariyaaa!". Kamar daga sama ta jiyo sautin amon muryarsa mai cike da wani irin yanayi wanda ba ta san yarda zata ce yake ba amma dai da alamun rauni a cikin ta dago kanta tayi ta hango ya sauko daga kan motarsa ya doso in da take da sauri ta juya za ta koma cikin gida domin ba zata iya tsayuwa dashi ba sosai take jin ta a wani mataki wanda ya canza mata komai nata yake yaki da natsuwarta yake haifar mata da abubuwa masu tsoratar mata da zuciya da gangar jiki. "Don Allah...". Tsak! ta tsaya ba tare da ta waigo ba jin abin da yace sosai taji wani abu a muryarsa wanda ya kara rikita mata zuciya da kwakwalwa. "Ban san mai zance miki ba, ban san abin da ya dace na fada miki ba wanda zai canza komai da komai a idanuwanki". Nisawa yayi yana mai dafe kansa da yaji yana wani irin juya masa kamar zai watsar dashi a kasa bai san abin da zai ce da ita ba bai san abin da ya dace yace da ita ba bai san ya akayi ya zo nan wajan ba bai san akan abin da kawo shi nan ba gashi dai ga Mariya amma shi a karan kan sa bai san mai zai ce mata ba. Sosai ta gane inda ya dosa sosai ta fahimci akwai abin da ke addabar zuciyarsa. "Kayi hakuri na san ban kyauta maka ba...". "Please Mariya mana". Ya yi saurin katse ta jin abin da take fadi sosai ya ji wani iri a zuciyarsa. "Ni ya dace na baki hakuri ni ne nayi miki laifi ni ne na aikata miki ba daidai ba afuwarki nake nema ba ban yi zaton kalamai na za su sanya ki ki tsane ni ba...ko da yake komai ya faru ni na jawa kai na don Allah kiyi hakuri". Wani irin nauyi taji kanta yayi mata sosai taji rashin dacewa sosai taji kunya ta kamata ace mutum kamar Huzaif yake bata hakuri ta ya ya hankali zai dauka anya kuwa ba wata manufa a zuciyarsa anya kuwa zata yarda da maganarsa domin ita tun haduwarsu ta farko ta raina wa a zancin sa sosai ta gane bai iya lafuza ba... "na san dole ki ji ba dadi a ranki amma duk da hakan ki daure ki yafe mani Mariya sosai da sosai na shiga tashin hankali a rayuwa tun haduwa dake na kasa sukuni komai nawa na rasa gane kan sa na sani kece...kece silar komai ya faru kuma na sani nine ban da gaskiya". "Na yafe maka Allah ya yafe mana baki daya ni dama ba kayi mani komai ba". Sosai ta gaji da maganganunsa shiyasa ta katse masa hanzari da amsar bukatarsa. Wata irin a jiyar zuciya yayi kafun ya dubeta da wani irin kallo. "Na gode sosai Mariya". Gyaɗa kai tayi kafun ta dago idanuwanta ta dube shi sosai taji gabanta ya fadi saboda wani irin kallo da taga yana yi mata sosai taji wani iri a ko ina nata da sauri tayi kasa da kai. "So Fine Boy waye wannan yaro mai kyau dashi". Ya fadi yana shafar kansa. "Kanina ne". Ta fadi a hankali sosai taji dadi da yabon da yayi wa Mu'azzam hakan ya kara rage haushin sa da take ji. "Don Allah bani shi mana mu gaisa". Ya fadi yana mai kasa da murya gami da mika mata hannu a hankali ta kwance Mu'azzam ba tare da komai ba ta mika masa wata irin runguma yayi masa gami da manna masa kiss a fuskarsa a daidai lokacin Mu'azzam ya buɗe idanuwansa yana kallon Huzaif murmushi yayi masa shima nan da nan ya wangale masa baki hakan ba karamin burge Huzaif yayi ba sosai ya shagala da kallonsa yana yi masa wasa har ya so mantawa da Mariya ma a wajan. Sai da tayi gyarar murya sannan ya dago ya dube ta da murmushi a fuskarsa. "Yana da kyau sosai ina son sa. Ya sunansa?". "Ibrahim amma Mu'azzam muke kiran sa". "Nice Name sunan nashi ya dace dashi sosai, ya fi ki kyau fa". Ya fadi da sigar zolaya Dariya tayi kadan kafun ta mika masa hannu. "kawo sa Umma ce ta aike mu fa?". Ba musu ya mika mata shi Kamar daga sama sai ga Hafsi tsaye akan su ta na duban su daya bayan daya a sheke Huzaif ya dube ta sannan ya dubi Mariya kau da kan ta tayi hakan da ta nuna sai ya karanci wani abu game da ita shima sai ya tsuke fuska kamar ba shi bane yake yiwa Mu'azzam wasa yanzu. Tsaki ta ja ganin sun ba banza ajiyar ta tayi cikin gidan tana kunkuni. "Sai anjima ma ko nagode". Ta fadi tana juyawa da sauri ya tsaida ita yana mai sanya hannu cikin aljihunsa kudi ya zaro masu dan dama ya mika mata. "Gashi ki sai wa Mu'azzam cakulat sannan don Allah in kin shiga ki gaida Umma". Irin kallon da ya ga ta na yi masa ne mai cike da tuhuma da ban so abin da kayi mani ba duk sai ya tsargu jikin sa yayi sanyi duk sai ya ji ya rikice ya rasa ma mai zai yi. Girgiza kai tayi kafun ta saki wani murmushi. "Uhmm rike kudin ka na gode sosai". Ta na fadin haka ta taka kafa da sauri ta bar wajan kallo ya bita dashi yana faman gyada kai kamar wani kadangare har takule a sabule ya mai da kudin sa aljihu ya jima a tsaye cikin nazari kafun ya ja kafarsa ya isa wajan motarsa ya bar unguwar cike da abubuwa masu girma da suka saka zuciyarsa nauyi. Duk abin da yake yi Mariya na laɓe a zauren gidan da tashige tana kallonsa sosai taji ya bata tausayi sosai take jin wani irin abu game dashi a zuciyarta musamman yarda ya baiwa Mu'azzam kulawa duk sai taji duk wani kunci da take ji game dashi yana bacewa daga filin zuciyarta gyaɗa kai tayi ta kara sa cikin gidan ta sayo tafarnuwar ta fito a hankali take tafiya zuciyarta na ta kawo mata abubuwa masu yawa suna samun gurbin zama a kofar gida ta ja burki ta tsaya tana gyara goyon Mu'azzam. Horn taji anyi mata a bayanta da sauri ta juya gabanta na faduwa duk a tunaninta Huzaif ne ya dawo amma sai ta ga akasin hakan Dr.Karami ne zaune cikin motarsa ya zuru kafafuwansa waje ya sauke gilas din yana kafe ta da idanu sai faman murmushi yake yi ita ma murmushi tayi tana mai yin kasa da kai. A hankali ya mike kan kafafuwansa ya karasa fitowa ya kulle motar yana takowa zuwa gareta har lokacin kanta na kasa "My Boy ya kake?". Ya fadi yana taba Mu'azzam shi kuma sai faman zillo yake yi alamun yana so yaje wajan sa sosai suka saba tsakaninsu sosai Dr.karami yake son Mu'azzam in dai ya zo gidan to tabbas Mu'azzam na hannunsa har sai ya tashi tafiya. "Ina yini". Ta fadi kanta a kasa bai kula ta ba illa kokarin zare Mu'azzam da yake yi a bayan ta ganin haka ya sanya ta kwance shi. Daukarsa yayi ya rungume shi yana mai manna masa kiss shikuwa sai faman Dariya yake yi. "me kika fito yi waje tare dashi da ranar nan?". "Umma ce ta aike ne sayan tafarnuwa". Kallon hannunta yayi ba tare da ya ce da ita komai ba ya fara taka kafafuwan sa zuwa cikin gidan domin ba ai masa shamaki ba Umma ta bashi dama ya dinga shigowa duk lokacin da ya zo ya daina tsayawa a waje. Mariya bin sa tayi a baya har suka isa cikin gidan bakin Kofa suka hango Hafsi baje tana cin awara tayi ɗaiɗai da kafafuwanta sai faman jan hanci take yi tana gumi alamun yaji yayi yawa ko kallon su ba tayi ba su ma ba su bi ta kan ta ba sukayi sallama dakin Umma su ka shiga bayan ta ba su izini. Bayan sun gaisa nan Mariya ta shiga korawa Dr.karami bayani akan tafarnuwar da ta sayo wa Umma dariya yayi sosai kafun ya numfasa. "Mariya iyayen tsari to ai ba wani abu bane tafarnuwa tana da amfani sosai a jikin mutum ba ta da illar komai ana so mutane suke amfani da ita sosai ko a cikin abinci ne domin magani ce kamar yarda kika ji Umma ta fadi don haka sai ki kyale tayi amfani da kayanta". Dariya Umma tayi mata itama dariya tayi tana mikawa Umma tafarnuwar. Shiru ne ya gifta tsakanin su na yan dakiku kafun Dr.Karami ya ja numfashi ya dubi Mariya sannan ya dubi Umma. "Umma dama akwai maganar da nake so muyi game da Mariya akan karatun ta ya kamata ace ta koma makaranta zaman ta hakan ba zai yuwuwa ba ya kamata ace a yarda take da kuruciyar ta ace tana makaranta yanzu". shiru Umma tayi tana gyaɗa kai sosai taji dadin maganar Dr.Karami domin tafi kowa son Mariya tayi karatu domin karatun Mariya abu ne mai muhimmanci a garesu dama al'umma baki daya sai dai WANI HANZARI ba gudu ba ba a nan gizo ke saƙar ba... "Umma karki damu nasan abin da kike tunani wannan duk ba wani abun da zai gagara ba ne ni aka ran kai na nayi alkawari zan dauki nauyin karatun Mariya tun daga yanzu har zuwa lokacin da zata kammala shi". Wani irin duban hanzari Umma tayi masa tana girgiza kai ba ta san wani irin mutum bane shi sosai ta fuskanci mutum ne shi mai yaƙana da alheri a rayuwarsa ba abin da ya hada su ba dangin iya babu na baba amma jibi yarda yake dawaniya da su tun daga lokacin da ta shiga matsalar cutar ta har zuwa wannan lokaci bai gajiya ba ga shi yanzu ya dauko wani gagarumin aiki wanda ya kamata ace su iyayenta ya dace ace duk sun yi sa. rintse idanu tayi wasu hawaye suka zubo mata ganin hakan ya sanya Dr.Karami saurin dubanta. "Don Allah Ki daina wannan kukan bai dace da ke ba sam! Addu'a ya kamata ace kin yi kawai Allah ya tabbatar da alheri". "Hisham ban san da bakin da zan gode maka ba kayi mani komai na rayuwa ba tare da kasan su waye mu ba nagode sosai Allah ya saka maka da alheri ya cika maka burukan ka na alheri ya kare maka rayuwa da zuri'a" . "Ameen Summa Ameen". Ya fadi yana duban Mariya wacce tayi kasa da kai tana faman hawaye sosai ya ji ba dadi a ransa ba zai iya cigaba da zama yana ganin hawayen su ba don haka ya mike ya na mai ajje Mu'azzam. "Zan tafi Sai gobe kuma in Allah ya kai mu zan zo domin yin abin da ya dace". Ya na fadin haka ya fice daga cikin dakin ya bar su Mariya shanye da baki suna duban junansu... *KAMALA MINNA*😎😎  [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA ASHIRIN. Dubansa take yi da wani irin yanayi na na raina wayonka da azanicin ka kafun ta kau da kai tana mai sakin guntun tsaki ta nisa cikin yanayi na haushi. "Ban san mai ya hau kan ba Dr.Erena sosai ka bani mamaki ban taba zaton kalaman nan za su iya fitowa ɗaga bakin ka ba ka dube ni up zuwa down ban yi maka kama da mai karamin tunani irin naka ba aiki na zo yi a wannan company ba zaman zance mara kan gado ba". Ta karashe tana mikewa kan kafafuwanta fuskar dauke da tsananin bacin rai sai dai kuma acan kasar ruhinta da zuciyarta ba haka bane domin kuwa murna take har da tsalle-tsalle Dr.Erena ya kusan fadowa komarta abin da ta jima tana KUDIRI da muradin tabbatarsa kenan. "Areef..". Da sauri ta daga masa hannu kafun ta dauki jakarta dake ajje kan table din Office din nasa. "Ya isa haka bana bukata ban so ka takura min, in kuma kace takura min zakayi wallahi yanzun nan zan rubuta maka takardar ajje aiki...". Da sauri ya mike jin abin da take fadi jikinsa har ɓari yake yi ya iso inda take tsaye ya kafeta da idanunsa da suka gama tafiya a duniyar Areefa. "No Please ba sai mun je wannan matakin ba...But Areefa ya kamata ki fahimce ni mana alkawari nayi miki komai kike so kuma ko me kike so ayi na miki alkawari...". Da sauri ta watsa masa wani kallo wanda yake kara rikita masa lissafi kafun ta tsume fuska. "Ban san ta ya zan maka bayani ka fuskanta ba Dr.Erena ban san da wani irin kalami zan yi amfani ka gane abin da nake nufi ba". Tana gama fadin haka ta fara taka kafafun ta ta doshi kofar fita zuciyarta cike da abubuwa masu matukar yawa. Shi kuwa shanye baki yayi yana kallonta har ta fice kafun ya ajje wani numfashi mai karfi ya koma ya zube kan daya daga kujerun Office din nasa. ****** *FIRST CLASS INTERNATIONAL SCHOOL GWADA* Sosai farinciki ke wanzuwa a fuskarta tun lokacin da Dr.Karami ya danko ta daga gida zuwa haɗaɗɗiyar makarantar da ya zaba mata zata cigaba da karatun ta. Zaune take zuciyarta falla da farinciki mara musaltuwa har da guntayen hawayen na farinciki duban Dr.Karami take cikin wani irin yanayi wanda ita kanta ta kasa tantacce matsayin da take ji ya samu a zuciyarta sosai take jin matsayi mai girma game dashi a filin zuciyarta sosai take jin komai na canzawa a duniyar rayuwarta a yau daya kadai sosai take hango mafarkinta zai tabbata na son karatu da ta jima tana rokon Allah ya bata damar da za tayi shi yau gashi Allah ya jeho mata Dr.Ƙarami mutumin da bata taba zaton za ta gan shi a duniyar mafarkin ta ba balle a zahiri amma gashi Allah ya kawo matashi ta hanyar da bata yi zato ko tsammani ba. Numfashi ta ja kafun ta dago kai ta na kallon Office din da ta baro shi a ciki shi da shugaban makarantar suna zantawa. Kamar daga sama taji an dafa mata kafaɗa da sauri ta dawo daga duniyar tunanin da ta fada dago kanta tayi ta sauke kan wata matashiyar yarinya wacce a shekaru za suyi kai daya sai faman murmushi take sakar mata cikin yake ita ma Mariya ta sakar mata da martani. "Sannu ko sunana Baseera Haruna Sa'eed ni sabuwar daliba ce da Dadyna ya kawoni yau ke ya sunanki". Mariya da ta saki baki da idanuwa ta na kallon ikon Allah sai yanzu ta kyafta idanu kafun ta sake murmushi tana motsa laɓɓanta cikin mamaki da wannan kanzagi da zalaka na wannan yarinyar sai kace ta tambaye ta saki baki sai ratata zance take yi kamar an kunna rediyo ana sauraron shirin INDA RANKA. "Karki damu haka nake shi kansa Dadyna aku yake ce mani wai na fiye surutu shiyasa yace kawai nafi dacewa na zama yar jarida". 'Kuma dai!' Mariya ta fadi a zuciya tana tallaɓe haɓa kafun ta nisa. "yo ai ni kin hanani ma cewa komai sai zuba kike yi dole dadynki yace dake Aku ke ba ki san ni ba nima ban sanki ba amma kin saki baki sai watso mani zancen ki ke kamar na tambaye ki". Da sauri ta caɓe. "Woohh ai na san ke ba mai cutar wa bace daga ganinki kina da kirki da natsuwa sosai da sosai domin dady yace in zan yi abokiya na samu mai natsuwa ba irina mai shegen surutu ba". Dariya sosai Mariya take yi har tana rufe bakin ta mamaki take yi da halin Baseera sosai da sosai taji lokaci guda taji ta kwanta mata rai. "to ni dai zancen ya tsaya nan naji abin da Dadynki yace yanzu dai ke a ina kike kuma aji nawa kike...". yarfar da hannu tayi tana mai yatsine fuska. "wai fa ss-1 nake daga makarantar da muka baro da yake dadyna ma'aikaci ne sai aƙayi masa canji aka kawo sa nan garin shine zai canza min makaranta wai sai dai a mai dani js-3 ki ji fa don Allah ai wannan ci baya ne kamar ni kuma fa ina da kokari sosai da sosai...". "Yaa Allah! Baseera wai don Allah bakin ki baya ciwo ne don Allah tsaya ki ja numfashi mana". Mariya ta tare ta tana mai kama hannunta ta na zaunar wa kan kujerar da take zaune a kai. "karki damu akan haka nima yanzu placement zan rubutu na tafi ss-1 kin ga kawai sai mu tafi tare...". Wata irin zabura tayi tana dariya. "da gaske ki ke don Allah to shikenan ma na hakura da fa balli na tayar nace ban yarda ba amma tun da kin ce haka zan zauna saboda ke my abokiya". "Yaa Allah Baseera Oh My God wai ke don Allah yaushe zaki yi hankali ne Yaa Allah!". Wata murya ce suka ji kamar daga sama tana fadin haka da sauri Baseera ta zabura tana dosar mutumin da yake tsaye nesa dasu hannayensa sarke a kirjinsa sai faman kallon su yake yi da yanayi na damuwa a fuskarsa. "dadyna zo ka ga my new ƙawa wallahi mai kyau da ita ga ta da natsuwa irin ƙawar da kace nayi...". Janyo ta yayi yana jan kunnan ta wata karamar kara ta saki. "Dady Please don Allah ba zan sake ba". "Ban san yaushe zaki girma ba Baseera ke ko gajiya ba kya yi da surutu haba mana! a ko ina sai kin nuna halin ki nikam zan ce ma na fasa saka ki a makarantar ba zan iya da rawar kan ki ba...". "wayyo Allah dadyna Please for give me I'll never do that again". Yanayin da ta marare ce taka langwashe murya ya sanya shi dungure mata kai yana murmushi halin Baseera sai ita duk yarda ta san zai sanya ka ki daukar hukunci akan ta ta sani. "Zo mije ka ga my New Ƙawa please dadyna". ta fadi tana jan hannunsa shi kuwa sai fizgewa yake yu amma taki dai nawa har sai da ya bi ta sannan ta daina magiya har zuwa lokaci Mariya na zaune idanuwanta akan su duk abin da suke yi tana kallo wani burgewa da sha'awa suke mata sosai da sosai taji Baseera da mahaifinta sun burgeta yarda suke kulawa da juna da nuna soyayya tausayin kanta take tana tuno nata mahaifin in da yana nan da shi ma haka zai nuna mata soyayya fiye ma da ta Baseera amma ina! hakan ya gagara ƙaddara ta rabata dashi rabuwar da ba ta san a wani hali yake ba ba ta san yaushe ne zai dawo duniyarsu ba su cigaba da rayuwa a tare a inuwa daya. Tsiwar Baseera ce ta dawo da ita duniyar zahirin ta daga ta tunani nisawa tayi taja murmushi kafun ta dubi mahaifin Baseera da yake tsaya yana dubanta. "Ina yini dady". Mariya ta fadi cikin muryarta mai sanyi da girmamawa a ciki. Sosai yaji ta burgeshi sosai yaji yana so su kulla ƙawance da yarsa ya lura akwai natsuwa da hankali a tattare da ita. "lafiya yau ya hakuri da aku mai bakin magana". Murmushi ta saki don ta fahimci in da ya dosa da maganar sa kasa tayi da kai tana mai amsa masa. "Dadyna ka ga ba ta fada min sunanta ba amma ni na fada mata". Baseera ta fadi tana mai duban Mariya da take kallonta fuskarta dauke da murmushi. "Yaa Allah! ta ya ya za ta fada miki bayan kin cika mata kunne da surutu Allah yasa ma tace ba za tayi kawancen ba...". "Dadyyy!". Baseera ta fadi da rigima a muryarta kamar zata fashe da kuka duban Mariya tayi cikin yanayi na mararecewa. "Please don Allah fada min sunanki kin ji in ba haka ba nace ba zan yi makarantar ba ma". Yanayin da tayi maganar da gaske take hakan ya baiwa Mariya dariya ganin da gaske take. "sunana Mariya Bello Gwada". "woohh so Fastastic Nice Name". Baseera ta fadi tana mai kambama sunan Mariya. Ya tsine fuska Mariya tayi kamar wacce aka tsikarawa allura da sauri Baseera ta ware idanu alamun tsoro tashiga tambayar ta lafiya mai ke damunta?. Girgiza kai tayi alamun bakomai amma ita kadai ta san abin da take ji tun da ta tashi yau take jin wani iri a jikinta kamar bata da lafiya lokaci-lokaci take jin cikin ta da mararta na murɗa mata sai taji kamar numfashinta zai dauke amma ba wanda ta fadawa haka sai dauriya da take yi taki bari kowa ya gane sai dai in ya motsa mata take cizon laɓɓanta har ya lafa. Miƙewa tayi jin mararta ta daure sosai tana faman cizon laɓɓanta sosai Baseera ta lura da haka da sauri tayi wa mahaifinta nuni da abin da Mariya take yi da sauri shima ya ware idanuwansa sosai akan ta kafun ya dafa kafadarta. "lafiya Mariya me ke damun ki ko baki da lafiya ne?". haɗe jikinta tayi waje daya ji take yi kamar kayan cikin ta za su zubo kasa da sauri ta durkushe kasa tana mai sakin numfashi da sauri-sauri hakan da Alhaji Haruna ya gani ya sanya shi firgita kadan da sauri ya kamo ta sosai yana mai duddubata Baseera dake tsaye kuwa jikinta sai faman ɓari yake yi idanuwanta lokaci guda suka kaɗa sukayi jajir. "Dady what is wrong?". Muryarta a raunane kamar mai son fashewa da kuka. "Mariyaaa!". Muryar Dr.Karami da karaɗe wajan lokacin da ya fito daga office idanuwansa suka gane masa abin da ya sanya shi faduwar gaba idanuwansa a warwaje da sauri yayi jifa da ledar dake hannunsa ya tako cikin sassarfa kamo ta yayi sosai izuwa lokacin har ta fara ficewa daga hayyacinta hakan da ya gani ya kara tsora tashi da sauri ya dubi su Baseera da Mahaifinta cikin yanayi na tuhuma kafun ya kau da kansa cak! ya dauke ta yayi hanyar ficewa da ita daga wajan hakan da suka gani su ma sai suka rufa masa baya wajan da yayi Parking ya isa ya buɗe gidan baya ya sakata ya rufe kafun ya dawo gaba ya shige duk abin da yake yi cikin yanayi na tsoro da fargabar abin da zai je ya dawo key yayi mata kafun ya fizgeta ya bar harabar wajan suma Su Baseera motarsu suka hau suka rufa masa baya. Wani clinic ya nufa da ita dake kusa da makarantar cikin sauri yayi parking ya zo ya sungume ta yayi ciki da ita ba wani bata lokaci aka amshe ta kayi emergency da ita sosai Dr.Karami ya shiga tashin hankali ba abin da yake tsoro illa wani abu ya samu Mariya bai san abin da zai ce da iyayenta ba bai san da wani ido zai kalle su ba bai san a me za su dauke shi ba fata yake yi Allah ya saukaka lamarin Allah yasa ba wani abu ne ya same ta ba. Kafadarsa yaji an dafa hakan ya san yashi tsayawa cak! daga Safah da Marwa da yake faman yi a kofar dakin da aka shigar da Mariya da sauri ya juye ya dube shi shima shi yake kallo kafun ya kau da kai bai san shi ba bai ma taba ganinsa ba amma sosai zuciyarsa ke nazarin mutumin domin kuwa abun da yafaru da Mariya a wajan su ne yana zargin su komai ya faru da ita su ne sila numfashi yaja kafun ya sake dubansa. "Mene ne hadinku da Mariya mai kuka mata?". Abin da ya fadi kenan muryarsa da zurfi a cikinta yana faman haɗe fuska waje daya. Sosai Alhaji Haruna yayi murmushi kafun ya bugi kafadar Dr.karami kadan. "Haba mana abokina karka zarge mu da komai a kan yar uwarka ba abin da muka yi mata...". "Ta ya kake so na yarda da maganarka...". Kafun ya dire ya jiyo muryar Baseera cikin kuka tana cewa 'Ina Mariya?'. Mamaki ne sosai ya cika sa ya shiga duban Baseera da alamun tambayoyi masu yawo sosai yake kallonta ko zai gane fuskarta amma ina bai ga alamun sanayya ba a tattare da ita kuma bai san taba balle yace yar uwar Mariya ce. "ya kamata ka fahimci wani abu a kan Baseera ba mu da niyyar cutar da ita kamar yarda ka ganmu a yau mu ma haka a yau mu ka fara ganin ka Baseera Da Mariya cikin wannan lokaci suka hadu na kawo Baseera zan saka ta a wannan makarantar to a nan ta gano Mariya har take cewa dani tayi ƙawa shine fa na zo ganinta har mun gaisa ma sai naga ta shiga wannan halin Dan'uwa karka zargemu da komai wallahi zuciya daya muke tare da ku ba mu da niyyar cutarwa gareku don nasan illar haka". Tun da ya fara magana Dr.Karami ke dubansa da idanunsa sosai ya fuskanci gaskiya a cikin kalaman sa sosai ya gane mutum ne mai kamal da hankali gami da natsuwa lokaci guda yaji kunyar abin da yayi domin kuwa Alhaji Haruna zai girme masa nesa ba kusa ba. Murmushi yayi yana sosa keya kafun ya dubi Alhaji Haruna. "Afuwan na tuhume ku akan abin da ban san ya yake ba kuyi hakuri Mariya amana ce a waje na dole in shiga yanayi in na ganta cikin wani hali". "kana da gaskiya hakan yayi daidai yanzu dai wani hali take ciki". Gƴaɗa kai yayi kafun ya nisa. "sun shigar da ita ciki domin dubata...". Bai kai ga karasawa ba likitan da ya shiga duba Mariya ya fito yana duban su kafun ya ba su hannun suyi musabaha yana mai duban su daya bayan daya har ya dire kallon sa ga Alhaji Haruna. "Kai ne mahaifinta ko?". Ya tambaya kafun ya dora. "karka damu tana lafiya lokacin ta ne yayi nasu na mata kuma bata saba ba shiyasa ta shiga wannan hali amma Alhamdulillah muyi settling din komai yanzu haka ta samu barci nan da 30mint komai zai zama normal". Hamdala sukayi su duka kafun Alhaji Haruna ya nisa. "Muna godiya Doctor sosai da sosai Allah ya bata lafiya". "Ameen.Yanzu dai zan muku last na magungunar da za a sai mata tana amfani dashi". Gyaɗa kai sukayi Dr.Karami shi dai shiru yayi yana mamaki yarda Alhaji Haruna ya zage yana nuna shine Mahaifi gareta ba tare da nuna eh da gaske ba 'yar sa ba ne hakan yayi masa dadi a rai lokaci guda yaji mutumin na burgeshi sosai da sosai. Ko da ya dawo daga duniyar tunani mamaki ne ya sake kashe shi ganin Alhaji Haruna yabi likita Office din sa sakato yayi da baki ya duban hanya kafun ya dawo da kallon sa wajan Baseera da ta zauna ta zabga tagumi hannu bibbiyu kamar wacce aka aikowa da mutuwar wani a dangin su duk bakin surutu ya mutu kamar ba ita ba ce aku a dazu. "Ya sunanki?". Dr.Karami ya fadi yana mai duban ta cikin yanayi na mamakin yanayin da ya ganta aciki kuma ya san duk a dalilin Mariya ne. Ba ta an sashi ba illa kallo da ta yi masa tana mai sauke numfashi mai kwari sosai. "C'mon Baby girl tell me your name...ko ba kya so ƙawancen da Mariya ne". Ba tayi niyyar ansa shi ba amma jin abin da yace ya sanya ta sauri dubansa da murmushin yake. "Please don Allah karka hana Mariya ƙawance dani sosai nake son ta a raina a lokaci guda naji ta burgeni kuma Dadyna ya na son ta ya yaba da hankalinta sosai da sosai". "Oya C'mon tell Now". Murmushi ta saki ganin yarda yayi mata cikin yanayi na wasa. "Baseera Haruna Sa'eed". Sosai yake dubanta yana tunanin in da ya san sunan mahaifinta sosai yake zaton ya san sunan amma ya manta a ina ne ya san haka gyaɗa kai yayi kafun ya nisa fuskarsa da murmushi. "Masha Allah to naji na amince kuyi ƙawance But...akwai sharaɗi kafun amincewar...". "Na yarda wallahi tell me". Ta fadi cikin yanayi na zagwadi dubanta yake yi sosai, sosai ya lura i Baseera irin mutanan nan ne masu barkwanci da wasa da dariya a ko ina suke. "ban da wasa in an fara karatu ina so ku hada kan ku waje gudu sosai nake so naji ana alfahari da ku a cikin makarantar nan". "Promise". Ta fadi tana mai dariya burin ta ya cika na samun ƙawa a lokaci daya daga zuwa makaranta. "hala tana nan tana yi maka halin nata na surutu kamar aku". Muryar Alhaji Haruna ta yanke musu hirar tasu Murmushi Dr.Karami yayi kafun ya dubi Baseera da ta cuno baki gaba alamun ba ta so abin da dady yayi mata ba. "Yaa Allah! Ai ba za tayi ba tayi mani alkawari dainawa in kuma ta cigaba ba zan barta ta cigaba da ƙawance da Mariya ba". "yawwa kayi mani daidai". "kai dady". Baseera ta fadi fuska a shagwaɓe har sai da ta basu dariya su duka. "ku tashi mu shiga mu duba ta ko?". Ya fadi yana mai dubansu ai kamar jira take cikin hanzari ta mike tayi hanyar shiga dakin har tana kokarin buge Dr.Ƙarami shi kam dariya abin ya bashi shikuwa dady dafe kai yayi kawai yana mai duban Dr.Karami yana mai masa nuna da ido yayi hakuri ba ta da hankali murmushi kawai ya yi yayi gaba. Kwance suka tadda ita sai faman sharar barci take yi kallo daya zakayi mata ka gane ta ji jiki a dan lokacin don har fuskarta ta fada sosai Dr.karami yaji wani iri a ransa ganin yanayin da Mariya take ciki ji yake yi kamar ciwon da yake jikinta ya dauko ya mai doshi nashi jikin bai son abin da zai sake taba mata rayuwa bai son abu ko ya yake ya rikita Mariya sosai yake jin tausayin ta sosai yake jin wani iri game da ita duk lokacin da take cikin hali na damuwa sosai yayi KUDIRI a zuciyarsa da ruhinsa da izinin Allah sai ya canza mata rayuwa sai ta ji dadin rayuwa sai taji dadin yan uwa sai ya zame mata yan uwan da take kwadayi a rayuwarta sai yayi iya kokarin sa don ganin ta fuskanci rayuwar 'yanci duk wani kunci da damuwa sun bar duniyar ta sai dai bai san ta yaya zai yi wannan aikin ba bai san wacce hanya bace da zai bi amma dai zai yi iya bakin kokarin sa don ganin rayuwar Mariya ta zama normal like others. Sai da suka shafe awa daya kafun Mariya ta farko sosai da sosai take duban su da idanuwanta da suke bude runtse idanu tayi ta shiga tunano abin da ya faru da ita wasu hawaye suka zubo mata a hankali ta ja numfashi kafun ta buɗe idanunwanta Baseera ta gani kusa da ita ta mai sakin mata murmushi ta sanya hannu ta dauke mata hawayen da suke zubo mata. "Sannu ƙawata". Ta fadi cikin yanayi na taushin murya da jajantawa. Ba ta ansa ba sai duban Dr.karami da tayi da ya tallaɓe haɓa ya zuba mata manyan idanuwansa masu firgita mata tunani gyaɗa kai tayi tana masa kallon tambayar me ke faruwa mai ya kawo ni nan?. Sosai ya gane abin da take nufi amma sai ya kau da kai domin bashi da bakin da zai iya cewa ga abin da ke faruwa da ita so yake yi sai sun koma gida komai a natse sannan sai suyi magana sosai da sosai. "ina ke miki ciwo Mariya?". Alhaji Haruna ya fadi cikin yanayi na tausayawa gyaɗa kai tayi alamun babu. "Masha Allah haka ake so Allah ya kara lafiya ko Mariya" Gyaɗa kai ta yi kawai sosai take hango karamin ci irin na wadannan mutanan daga haduwa amma sun yi mata abun da wasu nata suka gagara yi mata sun bata kulawa da duk lokacin su sun tausaya mata da halin da ta shiga sosai taji sun samu matsayi mai girma a zuciyarta sosai take hango martaba da karamci tattare da su bata da bakin da zata ce da su komai sai fatan alheri. Ba su jima cikin asibitin ba bayan dube dube da likita ya sake yi mata ya tabbatar da ba komai ya ba su sallama domin tafiya gida a tare suka fita Baseera da Dady su ka hau mota daya ba don ta so ba don cewa tayi sai dai ta bi Mariya gidan su amma Dady yace tayi hakuri zai kai ta da kan sa zuwa da yamma suna cikin wannan yanayin ne Mariya dake tsaye jingine da motar Dr.karami tana kallon diramar da ake yi da Baseera sosai taji wani abu a kafarta yana bin ta da sauri ta duba. "Yaa Allah! Jini". Ta fadi muryarta da karamin sauti da sauri ta dubi wajan da suke tsaye tana duban su a daidai lokacin Baseera ta dubeta ganin yarda tayi da ido ya sanya tambayar ta ko lafiya nuni tayi mata da kafarta da sauri ta iso gareta tana dubawa to da yake zata girmewa Mariya a shekaru sai ya kasance ta gane abin da ke faruwa kuma dama dazu taji abin da likita ya fadi da sauri ta dubi Dady da Dr.karami. "Dady muje da ita gida don Allah She need help please dady". Yanayin da tayi maganar sai ya sanya su duban Mariya da sauri don ba su gane akan me take magana ba. Da idanu tayi musu nuni tsaf! Su ka gane ita dai Mariya kanta na kasa cikin hanzari suka shiga motar su suka dauki hanya da yake ba nisa gidansu Baseera tafiya kadan sukayi suka isa Babban gida ne kallo daya zaka yi masa ka gane mai shi yana da rufin asiri sosai da sosai get ne babba mai ruwan blue sai ratsin gold da kayi masa Horn daya sukayi aka buɗe musu gabadaya suka shige ciki bayan sun yi Parking duk suka firfito ita dai Mariya duk a tsora ce take sai faman haɗe jikinta waje daya take yi da sauri Baseera ta kama ta sukayi cikin gidan a falo su ka tadda Hajiya Abida mahaifiyar Baseera babbar mace ce mai cikar kamala da mutunci sosai ta dubi Baseera fuskarta da tuhuma. "ba dai har kun dawo ba ina dadyn naki yake?". Tana magana ta na duban Mariya da take haɗe jikinta kanta a kasa duban Baseera tayi da kallon karin bayani. "later please Momy". Ta fadi tana zarcewa da Mariya in da dakin ta yake suna shiga ta zarce da ita Toilet duk wani abun bukata sai da ta tadanar mata kafun ta nuna mata duk yarda zata yi sannan ta fito ta bar ta a Toilet din ma'ajiyar kayan ta ta nufa ta buɗe wata doguwar riga ta fiddo gami da wani hijabi mai kalar pink da ratsin kalloli daban daban wanda suka karawa hijabin kyau sosai bakin kafcecen gadon ta ta ajje su sanna ta zauna ta na mai zabga tagumi mintina goma Mariya ta shafe a toilat kafun ta fito tana raɓe-raɓe kamar mara gaskiya da sauri Baseera ta mike ta isa wajanta. "dafatan kin yi yarda nace ko?". Gyaɗa mata kai tayi domin wata irin kunya ce taji ta lullubet sai sunne kai take yi kasa. "Uhmm Karki damu kin ji ko Mariya ba abin da zai sa me ki in Allah ya yarda". Kai kawai take gyaɗa mata a haka har ta taimaka mata ta kara gyara jikinta bata kayan da ta dauko mata ta saka da kanta ta gyara mata fuska ta baɗe mata jiki da wani lafiyayyan turare mai sanyin kamshi. Suna cikin kwalliyar ne Hajiya Abida ta shigo fuskarta dauke da murmushi tana duban Baseera. "dakyau Auta ta kin kyauta da wannan taimakon da kikayi dadyn ku ya fada min komai dake faruwa". Murmushi Baseera tayi ita kuma Mariya kasa tayi da kai don kunya. "'Yawwa Mariya kisan mi yanzu lokaci ne da ya kamata ki kula da kan ki sosai ban da wasan banza ko kule-kule kuma don Allah karki sake ki kasance mai yawan zama cikin maza ke 'ya mace yanzu girma ya kamaki dole kiyi taka tsantsan da rayuwarki domin abu kalilan zai ruguza miki rayuwa ba fata ake ba amma tunatarwa na da dadi in Allah ya yarda Allah zai kare muku rayuwa da sauran 'ya'ya mata masu wannan lokacin Allah ya tsare muku rayuwa ku duka kin ji 'ya ta Mariya". Sosai Mami tayi mata nasiha da tsoratarwa akan abin da zai rugaza mata rayuwa ba karamin dadi Mariya taji ba ta shiga mata godiya nan aka kawo mata abinci Mami ta saka ta gaba sai da ta ci sannan suka hada mata goma ta arzuki su ka rakota har falo in da Dr.Karami yake zaune da Alhaji Haruna ba karamin bugawa gaban Dr.karami yayi ba ganin Mariya ta sauya lokaci daya kamar ba ita ba ya shiga cizon laɓɓansa don tabbatar da Mariya ce ba wata ba wani murmushi ya sakar mata kafun ya mike bayan yayi wa su Alhaji Haruna godiya da karamci da sukayi musu har wajan mota suka rakosu nan Baseera ta sanar da Mariya anjima da yamma in sun taso islamiyya zata zo gidan su a haka sukayi sallama suka tafi zuciyoyin su fal da farin ciki mara musaltuwa. Tun da suka baro gidansu Baseera ba wanda yayi magana a tsakaninsu Mariya sosai ta haɗe jikinta waje daya kirjinta taji yana bugawa a hankali ba abin da ke yi mata yawo akai sai abin da ya faru da ita da kuma irin maganganun da taji Mami na fada mata wanda ta tabbatar haka abin yake rintse idanu tayi ganin abin take yi kamar almara kamar cikin mafarki ba gaske. A bangaren Dr.karami shima mamaki ne ya cika shi ko da yake in yayi duba da yanayin ta lokacin ta yayi a matsayin sa na likita zan iya gane haka wanda ma ba su kai shekarunta ba ma sun yi balle ita da yake zaton za tayi 16years. Da wannan tunanin da zuciyoyin su suke suka isa gida daidai kofar Gidan yayi Parking tsayuwar motar ne ya dawo da Mariya duniyarta da sauri ta dago kai dubi bangaren Dr.Karami da sauri tayi kasa da kai domin ita yake kallo a hankali ta sanya hannu ta buɗe kofar ta fice kamar daga sama idanuwanta suka hango mata abin da ya kusan sanyata sakin fitsari Huzaif ta hango zaune saman motarsa ya haɗe kansa da gwuiwarsa bisa alamu ya jima a wajan zaune da sauri ta juya ta dubi Dr.karami wani irin kallo ta ga yanayi mata mai cike da tuhuma sosai ta hango wani irin yanayi mai kama da bacin rai a fuskarsa kasa tayi da kai da sauri ta fara taka kafafunta wanda take jin su kamar za su narke sosai take jin kanta na wani irin juyawa kamar zai dare gida biyu duk taku daya in tayi sai ta ja numfashin ta da taji yana barazanar daukewa ba ta kai ga shig gida ba taji kugin tsayuwar mota da sauri ta juyo Dr.Aqeel ta hango yana fitowa daga ciki motarsa idanuwansa akan ta sosai ta firgita ganin wani kallo da shima yake yi mata wanda bata san da me zata fassara shi ba a ranta ta furta. "Yaa Allah! me ke shirin faruwa da ni ne?". Ai ba ta san lokacin da ta ja kafa tayi cikin gida ba sai faman haki take yi ba ta tsaya ko ina ba sai cikin dakin Umma ta baje kan katifar dake yashe cikin dakin sai faman sakin hirji take yi gabanta na faman bugu kamar zai tarwatse komai taji yana juya mata Umma da ke zaune ta shiga dubanta da mamaki da farko ba tayi zaton Mariya ba ce sai da ta kalleta sosai domin kayan da ke jikinta ba ta san ta da su ba tana kokarin yin magana ta tsinkayi sallamar Dr.Karami da sauri Mariya ta kara dunkulewa waje daya tana cusa kanta cikin hijabin dake jikinta gabanta na kara tsananta bugawa. Ko ta kan ta bai bi ba Umma kawai yayi wa bayani abin da ya faru mamaki sosai taji nan ta shiga yi masa godiya amma shi ina hankalinsa na kan Mariya wani kallo yake watsa mata ta gefen ido kafun ya dubi Umma muryarsa da sanyi. "Umma na mance shaf! in Allah ya kai mu gobe zan koma can wajan aikina domin hutun da na dauka ya kare ina muka fatan alheri sai na dawo". yana gama fadin haka ya mike saman kafafuwansa Umma kuwa sai faman sheka masa addu'a take yi da neman tsari. A haka ya fita ba tare da ya dubi Mariya ba baya ya ajje wa Umma bandir din kudi masu yawan gaske duk da zuciyarsa sai a zalzalar sa take yi ita kam Mariya ba a maganarta domin lokacin da taji abin da ya fadi ba ta san lokacin da hawaye suka wanke mata fuska ba wasu katangun tashin hankali suka rikito mata akai lokaci guda taji wani zazzabi na shirin rufe ta gabadaya ta kasa motsi jikinta gabadaya taji ya canza kamar ba na ta ba komai taji ya sauya mata a kankani lokaci tsoronta daya Allah yasa ba fushi yayi da ita ba ya yanke mata wannan danyen hukuncin mai barazanar tafiya da numfashim ta kuka take yi na zuciya idanuwanta sai zubda hawaye suke yi sosai take hango tashin hankalin da za ta shiga in ba Dr.karami ta dade a wannan yanayin kafun wani mugun barci yayi awon gaba da ita ya je fata wata duniya mai dauke da Dr.Karami wanda ta kasa tantace ta mene ne sannan ta kasa gane wata irin rayuwa ce suke yi sosai ta hango tashin hankali mutane uku take hangowa ko wanne kuma ita ya dosa da abu mai girma wanda ta kasa gane mene ne? *KAMALA MINNA*😘😘 [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA ASHIRIN DA DAYA. Tun ranar da Dr.Aqeel ya dauki kafarsa ya bar kasa najeriya shikenan natsuwar zuciya da ruhi suka gagari duniyar Mariya sosai ta shiga tashin hankali mara musaltuwa bata taba zaton zata yi k'ewarsa har haka ba bata zaton zuciyarta da gangar jikinta za su kasa sukuni har haka ba tayi kuka, kukan wanda take zaton zai rage mata raɗaɗi zuciya amma hakan bai yuwuwa ba sosai ta raya darurruka masu yawa cikin yanayi na damuwa da takomshin saƙar zuciya. Sosai takoma shiru-shiru magana ta za me mata wani aiki kato a duniyarta ba ta san ya kayi ta batawa ran mutumin da ya jikanta a rayuwa ba ba ta san mai yasa tayi gangancin haka ba bata san mai yasa a ranar da za su rabu ta barshi sa tukwuicin bacin rai ta sani da fushin ta ya bar kasan nan ta sani dole ya shiga cikin yanayi na bacin rai duk a dalilin ta ina zata gan shi ta bashi hakuri a ina zata ganshi ko ba a zahiri ta wanke laifin da ta yi masa ta sani sosai yayi mata nisa nisan da ba ta da damar da zata je in da yake har karshen rayuwarta in bashi ne ya dawo ba ya tadda ita tunanin ya ta'allaka ne a yarda za t rayu dashi a zuciyarta wanda ba ta san adadin lokacin da zai dauka kafun ya dawo ba sosai take hango gangancin da tayi na bata damar da ta samu. Haka ta cigaba da rayuwa cikin wannan yanayi da tunanin Dr.Karami lokaci mai tsayi cikin duniyarta haka ta cigaba da zuwa makaranta tana karatu da tunanin Dr.Karami a ranta da ruhi dama duniyarta baki daya. Mutum daya ce take samun damar da take zama tana zantawa da ita har ta rage mata damuwar dake addabar zuciyarta sosai Baseera ta taka muhimmiyar rawa a duniyar Mariya sosai take nuna mata rashin dacewa ga halin da ta je fa kanta duk yarda zatayi don ganin ta rage mata tunanin abin dake dawainiya da Mariya tana yi sosai take hanata zaman shiru kulli-yau min in dai basu da lesson to tabbas zaka same su zaune waje guda suna bitar karatun su domin Baseera ta hakikance haka ne kawai zai rage abubuwa da yawa a duniyar Mariya da suka addabe ta. A bangare guda kuma Dr.Aqeel da Huzaif suma sosai suke saka ta cikin halin rashin kwanciyar hankali domin ta hakikance a ta dalilinsu komai ya faru da ita tsakaninta da Dr.Karami sosai take jin tashin hankali a duk lokacin da suka kwaso jiki suka zo gareta bata san abin da suke nufi da ita ba sosai take ganin suna takura mata domin kuwa laifin komai da komai da ya faru akan su ta daura su ne silar faruwar komai. Ko dai dai in tayi duba ta wani fannin duk wanda ya zo a tsakaninsu tana kula su hakan kuma na kara tuna mata da Dr.Karami tana ba su lokaci sosai da sosai domin Dr.Aqeel ba abin yadawa bane shima ya taka muhimmiyar rawa a duniyar rayuwarta sosai da sosai ba za ta yi masa halin dan'adam ba mai mai da alheri zuwa akasin sa. Haka shima Huzaif duk da tabon da yayi mata a zuciya hakan bai sa ta watsar dashi tun da ya nuna nadamarsa akan abin da yayi amma kuma ba hakan bane ya sanya ta tsayawa dashi har ta bashi lokacin ta illa soyayya da yake nunawa kaninta Mu'azzam soyayya ce mai girma a tsakaninsu gami da shakuwa sosai da sosai yake bashi kulawa yake tattalin sa kamar dan'uwansa na jini hakan ba karamar rawa ya taka ba har Huzaif ya samu matsayi a filin zuciyarta. ba ta san wata irin ƙaddara bace take yawo da ita a duniyarta a duk lokacin da ta tuno abubuwa da suke ta faruwa da ita a filin rayuwarta sosai take hango tashin hankali mai girma nan gaba duk ranar da Dr.Karami ya duro kasar nan. ***** "Nikam ina ganin Bariki 'ya duk idanuwanta sun gama buɗewa tana kallon mutane ɗai-ɗai kamar tsararrakin ta ni ban san wani tsohon makiri bane da wannan danyen aiki in ban da son sani da kalan-dangi da neman mai da yariya karamar yar duniya me nene haka kullum yarinya kenan da tsukanken wando da guntun hijabi tana zarya a hanya kowa ni kare da doki suna kare mata kallo". Goggo Marka ce take fadin haka tana tafa hannu a daidai lokacin da Mariya ta dawo daga makaranta jikinta sanye da Uniform riga da wando sai hijabi wanda iyakarsa kirjinta. Tun da Mariya tafara daukar kafarta zuwa makaranta tun daga wannan rana Goggo Marka take debe mata albarka akan cewa iskanci kawai da duniyanci ya sanya aka saka ta makarantar yahudawa yarinya sai kara girma take yi tana buɗewa kowa ni namiji sai kallon ta yake yana haɗiyar yawu. Ba karamin tashin hankali Mariya tashiga ba a ranar da taji mugun nufin da Goggo Marka ke jfanta dashi tayi kuka kuka mai amsa sunansa kuka Umma ita kanta tayi bakin ciki mai girma sosai zuciyarta tashiga tashin hankali jin mugun nufin da ake jefar 'yarta da shi a ranar ta so ta hana Mariya zuwa makarantar amma zuciyarta ta hanata tana mai gargaɗin ta akan sabawa alkawari da kuma rashin baiwa Dr.karami muhimmancin abin da yayi musu na alheri sosai tayi duba akan ilmi tasan ilmi na da matukar muhimmanci a duniyar rayuwar 'yarta sosai karatun da tayi zai taimaka mata a fannoni masu yawa a wannan zamanin da ake ba wai ita kadai Mariya ba har da su iyayenta da al'umma a duk ranar da ta zama wani abu a filin duniyar nan a dalilin karatu tasan za suyi alfahari da ita sosai da sosai. Ta sani dole ne ta jajirce sannan ta kau da kunnuwanta ga sauraron duk wani mugun furuci da za a fada mata ita da 'yarta dole ta rarrashi zuciyarta dole ne ta cigaba da yi ma 'yarta addu'a sannan ta kara mata karfin gwuiwa ta nuna mata amfanin karatu a duniyarta da su iyayenta dama Al'umma gabadaya ita dai fatanta a kullum Mariya ta tsare rayuwarta da martaba gami da darajarta ta dage wajan karatu sosai da sosai duk wuyarsa da wahalarsa zata ga amfaninsa nan gaba sosai da sosai domin a yarda suke yanzu karatunta zai matukar taimaka masu nan gaba sannan ta kara tunatar da ita cewa ta dube su da rayuwar da suke yi ta tabbata in da sunyi karatu a zamaninsu ba a za su fuskanci kalubalin rayuwa har haka ba ko ma za su fuska to ba zai yi tsauri haka sosai da sosai ba. Huɗubar Umma sosai ya samu waje a filin zuciyar Mariya ta ajje waje na musamman. Sosai take jin tausayin iyayenta na kara samun fili mai girma a zuciyarta da ruhinta sosai take hango irin rayuwar da suke gudanarwa tana hasashe kafun zuwanta duniyar nan ta sani sun fuskanci KALUBALE sosai da sosai in tayi duba da yarda auren iyayen nata ya kasance a yarda take samun labari sosai suka shiga tashin hankali kafun tabbatar auren iko na Allah ne kawai yayi aiki a tsakanin iyayensu har suka bar su suka auri junansu. Domin sosai ake fuskarta matsala tsakanin Fulani iyayen Habeeba da manoma iyayen Bello sosai rashin jituwa ke tsakaninsu amma sai Allah ya kulla soyayya mai girma tsakanin 'ya'yansu wanda haka sam bai yi musu dadi ba su iyayen musamman ta bangaren iyayen Habeeba domin AKAN SO da take yi wa Bello ta zabi kin bin iyayenta domin da rigima tayi rigima abu yaki ci yaki cinyewa sosai suka fara kokarin haɗe kayan su domin canza mazauni nan Habeeba tayi tsalle ta dire ta nuna ita ina ba za ta bi su ba komai za suyi mata kuwa tana tare da Bello gani take in aka raba ta dashi to tabbas zata iya rasa rayuwarta sosai iyayenta sukayi fushi da ita har ya kai ba sa yi mata magana ganin da sukayi da gaske take sannan da ban baki da mutane suke ba su hakan ya sanya su barwa Habeeba auranta akan kuma komai yasa me ta kar ta sake ta tako kafa in da suke domin kuwa duk tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa kan doka a ranar da aka daura auren Habeeba da Bello a ranar iyayenta suka bar garin Gwada gabadaya zuciyoyin su cike da abubuwa marasa dadi su yi KUDIRI a ran su ba za su sake takowa zuwa wannan garin ba har gaban abada. A lokacin da akayi auren Bello mahaifiyarsa bata raye mahaifinsa ne kawai yake duniya sai matarsa Marka wanda tun lokacin ita ce take rura wutar komai domin sam bata kaunar auren ta tsani Bello da uwarsa domin a tunaninta shi ne ɗa namiji a gidan kuma shi ne magaji ita kuwa 'yarta daya Zainabu wanda suke kira da Abulle Abulle macece mai hakuri bata biyo halin mahaifiyarta ba domin sosai take bakin cikin duk abin da taga mahaifiyar ta ta nayi wa su Bello Abulle ta riga Bello Aure domin tun tana shekaru sha biyar aka auren da ita tun da tayi auren bata taba haihuwa ba har akayi bikin Bello lokacin da Bello shima ya tare a nan gidan su sun jima kafun ita ma Habeeba ta samu ciki wannan rashin samun ciki sai ya buɗe wa Goggo Marka katon filin tsula rashin mutunci ga Habeeba tana mai aibata ta wai juya ce bata haihuwa kila ta gama yawon bin mazan ta acan rugarsu ta gama zubda kwayayen haihuwarta a layi wajan tallar su ta gado shine aka likawa Bello sosai take jin bakin ciki da takaici sosai ta so yin dana sanin auren Bello amma in ta tuna irin HALACCI da yayi mata ya nuna mata so da kauna ya tattale ta ya za me mata MIJIN MARAINIYA sai taji a ranta za ta iya zama dashi da ko wani irin hali ne ko da kuwa Goggo Marka za ta dinga yankar naman jikinta ta miya dashi. Ba karamin tashin hankali Habeeba ta fuskanta ba a tsayin shekaru biyu da tayi a gidan auranta sosai duk hakurin ta da kai zuciya nesa hakan bai hana ta shiga matsananciyar damawu ba duk da bata gayawa Bello abin da ke faruwa tun ba ya ganewa har ya zo ya na fuskanta ya yi bakinciki ya nuna bacin ransa amma mahaifinsa ya dinga ba shi hakuri akan kar ya damu wata rana sai labari. A na cikin wannn tataburzar ciki ya bayyana jikin Abulle Innalillahi wa inna ilaihir raji'una. Ina wuta Goggo Marka ta saka Habeeba nan fa ta sake bude sabon shafin gori da aibatawa bakaken maganun kuwa ba a magana a lokacin Habeeba ta ga tashin hankalin da bata yi tsammani ba domin kuwa Goggo Marka zuwa tayi da kanta tun cikin na wata bakwai ta danko Abulle ta kawo gida bayan an sha dirama in da Abulle tace ba in da zata je a bar ta gidan mijinta ita kuwa ta dire tace bata san zance ba haihuwar farko ce dole sai taje gida GOYON CIKI ban dan ta so ba haka ta kwaso jiki ta zo gida bayan mijinta ya amince mata ganin da yayi Goggo Marka na shirin birkita musu rayuwar auren su. Tun da Abulle ta dawo gida fa nan Aiki ya cewa Habeeba Salamu alaikum domin komai na Abulle ita ke yin sa ba abin da aka dauke mata hakan bai dame ta ba domin Bello ya bata baki akan cewa tayi kwana nawa ne Abulle zata koma gidan mijinta a haka har ta haihuwa inda ta samu ɗa namiji nan wata sabuwar duniyar habaici da cin mutunci ta buɗe akan Habeeba haka zata shiga daki tayi kukanta ta godewa Allah duk abin da ke faruwa Abulle na sa ne wani lokacin haka za ta faki idon Goggo Marka ta fada dakin Habeeba tai ta bata hakuri akan abin da ke faruwa domin har ga Allah tana jin bakin ciki da takaicin abin da ake yiwa Habeeba sai dai bata da damar hanawa in tayi magana haka Goggo Marka zata ta surfa mata zagi wai bata kishin kanta sannan ai Habeeba bata da amfanin komai a gidan tun da ba haihuwa take ba sai dai taci ta kwanta tayi kashi. Sai da Abulle tayi wata biyu cur! san nan ta koma gidan mijin ta a dan tsakanin Habeeba ta samu sa'idar aiki. Shekarun Abulle ashirin da Haihuwa ta sake samun ciki a lokacin ita ma Habeeba Allah ya taimake ta ya amsa du'a'in ta ya bata na ta rabon. Yaa Allah!. Ku zo ku ga murna wajan Habeeba da Bello da Mahaifin Bello wanda a lokacin girma ya kama shi sosai da sosai. Ita kuwa Goggo Marka ji tayi kamar ta hadiyi zuciya ta mutu don bakin ciki da takaici haka tana kallo Habeeba tayi rainon cikin ta da taimakon mijinta har ta sauka lafiya ta samu 'ya mace hakan yayi wa Goggo Marka dadi sosai domin haihuwar mace da akayi ta san ko ba komai dai ai an rage mugun abu in da namiji aka haifa ai da ta shiga uku. Satin su daya ita ma Abulle ta haihu ita ma dai 'ya mace ce. Ranar su aka sanyawa yarinya Mariya ita kuma Abulle aka saka ma 'yar ta ta Hafsatu. Tun daga wannan lokacin zama dai ya ki dadi a tsakin Goggo Marka da Habeeba har zuwa lokacin da su Mariya suka isa Yaye a lokacin Goggo Marka ta dauko Hafsatu da sunan yaye ta tun daga lokacin ta zama 'yar gidan ta sosai ta sargarta ta da sunan wai gata ba ta jin kunyar uban kowa tun tana karamar ta ta iya zagi da dukan mutane ba yarda Abulle bata yi ba domin ansar 'yarta ganin irin tarbiyar da ake yi mata Goggo Marka ta hau ta dire akan ba wanda ya isa ya rabata da Hafsatu wannan shi ne silar sangartar Hafsatu sai ta ga dama take zuwa wajan iyayenta ko taje to da rigima suke rabuwa da uwarta ta dawo tana kuka haka Goggo Marka zata zari mayafi ta je har gidan Abulle tayi mata rashin mutunci ta dawo gida. Shekarun Mariya Hudu Allah yayiwa kakanta Mahaifin Bello rasuwa sakamakon gobara da ta kama gidan duk kan su ba sa nan shi kuma jikinsa yayi nauyi sosai da sosai ko tashi bai ya iyayi haka yana kallo wuta ta kama shi ba shi da halin taimakon kan sa. A ranar sun ga tashin hankali a gidan domin komai ya kone ba abin mamora gabadaya wannan shine silar fadawarsu kangin rayuwa su ka fuskanci kunci sosai ya kasance abin da za su samu su ci ma sai Bello ya fita yayi buga-buga domin dama sana'ar tambobi yake yi to duk gobara ta lamushe jarin d kuma sauran dambobin da yake kiwo cikin gida. Wannan kenan. ******** Sanye take da bakar jallabiya mai dogon hannu wanda ta dan kamata jikinta kadan sai hijabi mai kalar pink sai fulawowi masu kaloli da suka karawa hijabin kyau sosai tayi wa kayan kyau ba wai su sukayi mata kyau ba ba wata kwalliya tayi ba a fuska ba domin Mariya sam ba irin matan nan ba ne masu son kwalliya in kuwa ka ganta da kwalliya to tabbata Baseera ta zo gidan ko kuma ita taje gidan su. Bayan ta gama shirin ta dubi Umma dake sauyawa Mu'azzam wando. "Umma ni na tafi sai na dawo". Ta fadi tana mai daukar jakar Islamiyyarta dake rataye. "Allah ya kiyaye hanya a kula sosai Mariya Allah ya bada ilmi mai amfani a dahe da karatu kin ji karatu yana bukatar jajircewa da mai da hankali akan abin da ake koya wa". Murmushi Mariya tayi tana mai gyaɗa kai a kullu-yau min in zata tafi makaranta maganar Umma kenan na nuna son ta kula da kanta kuma ta mai da hankali akan abin da taje koya har ta hadda ce maganar ta ta wanda ta samu fili a zuciyarta ta ajje ta kuma tayi Alkawari in Allah ya yarda za ta yi abin da Umma ke so ta ga ta yi. Da wannan tunanin ta fice daga dakin bayan ta jawa Mu'azzam hanci da yake ta faman kallon ta dariya ya saki ita ma mai da masa tayi sannan ta fito daga cikin dakin. Ta na cikin saka takalmin ta ta tsinkayi muryar Goggo Marka. "ina ganin lalata nikam wai sai a zage ai ta nuna wa mutane Allah a baki zuciya kuwa ta fir'auna ce yanzu in ban da kuturun kinibibi Hafsi ji be ta don Allah ta zabga doguwar riga har da zabgegen hijabi an rakito jaka wai za a karatun addini bayan an gama tambaɗewa a waccan boko jahanna ma din wai mu za ayi wa BIRI BOKO". Tsaki Hafsi tayi daga in da take zaune ta mimmike kaf kamar sabuwar 'yar kaciya sai faman kai noma bakin ta take yi. "Uhmm yo Goggo wani dare jemage bai gani ba ai sai na mutuwarsa ai mu tuni muka gane barno ba gabas take ba balle a juyar mana da alkibla kawai kallon mutum muke". Ta karashe tana sake yanko katuwar lomar taliya da taji yaji da mai har canza kala take yi kallo daya zakayi wa taliyar kasan an kashe mata kuzarin ta da barkono. In da sabo Mariya ta saba da irin wadannan habaice-habaicen don haka ko ta kan su ba ta bi ba ta na saka takalminta ta kama hanyar ficewa daga cikin gidan. "Hehehehe wai mu za a nuna wa bariki". Fadin Hafsi tana daukar kofin ruwa tana kai wa bakin ta gabadaya ta gama hada gumi kamar mai jego a lokacin zafi ta sha kunun kanwa. Zuciyarta sosai ta kuntata jin abin da Hafsi ta fadi akan ta a duniyar nan ba abin da ta tsana irin ace da ita 'YAR DUNIYA ko 'YAR BARIKI sosai take jin zuciyarta na kuna da zafi... "Mariya!". Kamar daga sama taji amon muryar ko ba a fadi mata ba ta gane ko waye in hadda ma ake akan muryar mutum ita kam! ta hadda ce. Tsayawa tayi ba tare da ta juyo ba tana jin takusan har ya iso in da take tsaye ya zo ta gabanta ya tsaya hannayensa harɗe a kirjinsa sosai yake kallon ta da duk idanuwansa sosai ya karanci akwai abin da yake faruwa da ita mara dadi daga cikin gidan kafun fitowarta ga idanuwanta sun kaɗa sun yi jajir numfashi ya ja mai girma kafun ya kau da idanunsa yana jin wani iri game da ita a zuciyarsa wanda har zuwa wannan lokacin ya kasa yarda da hakan sai fafatawa da zuciyar tasa yake yi akan kalubalantar ta akan abin da take sanar dashi. "Me ya same ki Mariya?". Ya fadi idanuwansa sosai a fuskarta da kallon tuhuma. Kasa ta karayi da kai tana mai girgizawa alamun babu komai a zuciyarta kuwa ba abin da ke kona mata ita sai kalaman Hafsi sosai ta tsani taji an jona mata rayuwar duniyarta da bariki ta tsani haka amma ita kuwa Hafsi ta mai da mata rayuwa kamar wacce take zaman kanta ko wacce aka ce je ki kya gani in dai duniya ce. "haba mana Mariya dake fa nake". Ba ta son tsayawa bata son bata lokacin ta tana bukatar ta isa makaranta da wuri. "Ba komai kawai dai yau na tashi ne bana jin dadin jiki na". Ware idanu yayi yana dubanta cikin yanayi na tausayawa kafun ya ja numfashi. "Amma kuma a haka zaki tafi makaranta kin san bakya jin dadi ya kamata ace kin sha magani kin kwanta". maganar ta fara gundurarta don haka ta dago idanuwanta ta dube shi sosai kafun ta kau da idanunta ba ta so suna hada idanu da Huzaif sosai take jin wani iri a zuciyarta da duk kan gangar jikinta sosai take hango wasu abubuwa masu girma cikin ƙwayar idanuwansa wanda ta rasa da me zata danganta su. "ba wai bani da lafiya bane, kawai dai yanayin garin ne yau gabadaya naji shi ba dadi". Ta karashe tana mai daga kafafuwan tana wuce wa. "Sai anjima". Ta sake fadi bayan ta gota shi tana cikin tafiyar cikin yanayi na rashin armashi ta tsinkayo muryar Hafsi na daka mata kira kiran da taji shi har tsakar kanta gabanta taji yayi wani irin bugawa kamar zuciyarta zata faso kirji ta fito. Da sassarafa ta iso gareta fuskarta ba yabo ba fallasa ta mika mata hannu. "Bani abin da kika dauka inji Umma". Duban rashin fahimta Mariya ta shiga yi mata mamaki ya cika mata zuciya akan abin da taji tace da ita to mai ta dauka mai Umma zata aiko Hafsi ta amsa a wajanta mai yasa tun kafun ta fito ba tayi mata magana ba sai bayan ta fito ta ya ya tasan tana tsaye kofar gida bata wuce ba har zuwa wannan lokacin?. Ware idanunta tayi sosai akan Hafsi da ta mata kerere akai sai faman yatsine baki take yi kamar ta ga wani abin kyankyami a hankali ta shiga motsa bakin ta cikin rashin abin cewa. "Ban gane ba". Ta fadi bakin ta na rawa sannan tana juyar da kallonta zuwa Huzaif da ya harɗe hannunsa yana kallon su gabanta taji ya sake faduwa domin ta gama yanke hukuncin akwai kullin da Hafsi ke kokarin yi mata domin tsinka ta a gaban Huzaif ba yau bane ranar farko da ta fara zuwa in da take tare da Huzaif in ya zo wajanta tana neman shafa mata bakin fatti ta tabbata yau nasara take hangowa a idanun Hafsi... "Kudin da kika dauka ta ce ki bani". 'Innalillahi wa inna ilaihir raji'un Yaa hayyu ya kayyum'. Ware idanu tayi sosai tana duban Hafsi da take jin kalaman ta kamar saukar aradu akan ta sosai ta hango tsabar kullin zarge a idanunwanta yarda take yawo da idanuwanta da motsa baki sai ka rantse da Allah gaskiya ne ga hannu data turo mata alamun ta ba ta kudin ji tayi kamar kasa ta tsage ta fada ciki don takaici da bakin ciki sosai taji a jikinta Huzaif na kallonta kallon da ba ta san wani yanayi ya ajje shi ba ta sani kallon wata iri yake yi mata ta sani yanzu haka a zuciyarsa ya yarda da maganar Hafsi da ta zo dashi kuma ta sani yanzu haka kallon tuhuma yake yi mata kuma wacce bata da GASKIYAR RAYUWA cikin duniyarta. "Hafsi kudi fa ki kace ita Umma din ta ce ki biyo ni ki amshi kudi?". Mariya ta fadi muryarta na karyewa da wani irin yanayi mai girma da tashi a hankali acikinsa wata irin sarawa taji kanta nayi kamar zai rabe gida biyu a hankali ta kai hannunta ta dafe kan. 'Yaa Allah'. "Malama ni fa 'yar aike ce ba wai ni nayi gaban kaina ba don haka ko ki bani ko kuma ki fada min abin da zan fada mata don cewa tayi in amso mata kudin ta in ba haka ba kar in sake in dawo domin sai ta bata min rai". 'A'uzubillahi minal shaiɗanin rajim'. Mariya ta fadi can kasar zuciyarta da ruhi wata irin juw ta ji ta na daukarta tana kokarin dire ta da kasa da sauri ta dubi Hafsi izuwa lokacin idanunta sun tara kwalla sosai take kallon ta da yanayi na baki yi min adalci ba ba ki kyauta min ba. Amma ita sai faman kau da fuska take yi tana kara tafke ta alamun ba wasa. "Wai shin me ke faruwa ne?". Kamar daga sama ta tsinkayi muryar Huzaif ya na fadin haka 'Yaa Allah' Mariya ta sake fadi ita kadai take jin abin da take ji a zuciyarta sosai take cikin tashin hankali wanda bata taba zaton ƙaddara za ta dauko mata ta kawo mata ba kuma da ta tashi dauko mata sai ta jeho mata Hafsi dauke da makirci ta zo ta dire mata a gaban Huzaif da yake mata kallon mutunci da mutuntawa. "Kudi ta dauka shi ne aka ce in biyo ta in ansa shi ne fa ta tsaya tana min yawo da hankali bayan kuma ta san ita ce ta dauki kudin". Muryar Hafsi ta karaɗe kwanyar Mariya da kunnuwanta da karin bayanin da take yi wa Huzaif wanda ta tabbata hakan zai kara mata wani bakin fatti a zuciyarsa. "Hafsi!!". Mariya ta fadi da sauti kafun ta dago jajjayan idanuwanta tana mata wani irin kallo na ban kiyi mani adalci ba. "Mariya". Taji Muryar Huzaif wani irin yankewa taji gabanta yayi a hankali ta juyo da kallonta zuwa gareshi sosai ta hango kallo wanda ba tayi tsammanin shi za ta gani ba kallo ne na rauni da tausayawa ta hango cikin idanuwamsa sai faman gyaɗa kai yake yi alamun tausayawa. "wuce ki tafi makarantar ki karki bata lokacin ki". Abin da taji ya fadi kenan da sauri ta ja jiki ta tafi zuciyarta na yi mata zafi da raɗaɗi sosai taji abin da Hafsi tayi mata ya taba mata zuciya ba kadan ba amma abu daya ya sanyata tafiya shine ganin irin kallon da Huzaif yayi mata wanda ba tuhuma ko zarge a cikinsa amma duk da hakan zuciyarta ta yi matukar kaɗuwa da faruwar wannan lamarin a gaban sa da wannan tunanin ta bar layin nasu. Huzaif da yake kallonta ganin ta kule ya juyo ya dubi Hafsi da tayi masa ƙyar da idanu tana kallonsa kamar wanda ta ga sabuwar halinta a duniyarta. "anshi ki kai wa Umma din sannan ki ce mata ba Mariya ba ce ta dauki kudin domin an duba ba a gani ba a dai sake duba cikin gidan a in da aka ajje su". gudar duba ce ya zaro ya mikawa Hafsi a dan kuntace ta ansa ba haka ta so ba ta so ace Huzaif ya ci mutuncin Mariya sosai a gabanta hakan zai fi mata komai farin ciki kwaɓa tayi tana mai juya duba dayar a zuciyar ta ce "raba mugu da makami ibada ne". Wani kallo ta jefawa Huzaif da wani irin yanayi kafun ta ja kafafuwanta ta koma cikin gida ranta fes ta sani dole zargi ya dalsu ko ya ya ne a zuciyarsa musamman irin kallon da ta ga yana yiwa Mariya da kuma irin muryar da yayi amfani da ita wajan yi mata magana. A hankali ya isa motarsa ya buɗe ya shiga yana jin wani irin sarawa da kan sa ke yi kamar zai rabe guda biyu don tsananin kaɗuwa da yayi da abin da ya faru yanzu duk da dai zuciyarsa ba wai ta amshi lamarin bane da gaskiya amma ya ji rashin jin dadi a zuciyarsa. Da wannan tunanin ya ja motarsa ya bar unguwar zuciyarsa fal da tunanin Mariya gami da damuwa da yanayin da ya ga ta shiga lokaci guda... *KAMALA MINNA*😘😘 [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA ASHIRIN DA BIYU. Sosai da sosai zuciyar Mariya ta taɓu akan abin da Hafsi tayi mata na kulla sharri ba abin da ke kara sanya ta cikin bakin ciki in ta tuna kamar yarda ta tsinka ta a gaban Huzaif wanda sam ba ta so haka ba inda ta san abin da Hafsi za tayi mata kenan da bata tsaya ta saurare ta ba balle ta saka mata CIWON RAI. Haka ta je makaranta har ta gama zaman ta ba tare da ta fahimci abin da aka koyar da su ba da wannan yanayi aka ta so su ta yo gida gabanta na tsananta bugu ba ta san ya Umma zata karbe ta ba, ba ta san da wata irin fuska zata kalle ta ba in abin da Hafsi tayi mata ya tabbata tabbas zata shiga yanayi mai taba zuciya sosai da sosai tana tsoron fushin Umma gareta sosai take tsoron abin da zai je ya dawo ta sani wannan halin da Hafsi ta jona mata yana cikin abubuwan da Umma ta tsana tsana kuwa mai tsanani domin a kullu yau min in tana yi mata magana akan abin da ta tsana dauke-dauke na sahun farko musamman akan abin da ba naka ba kuma ba tare da sanin mai shi ka dauka ba. Sosai zuciyarta tayi rauni wasu hawaye masu zafi da taba zuciya da ruhi ta ji suna sauka saman fuskarta sosai take jin zafin su a fatar fuskarta tana jin wani raɗaɗi mai ciwo na bin ko wani sashi na jikinta. Hannayenta ta saka duk biyun ta na shafe fuskarta ba abin da take ai yana wa a zuciyarta sai. 'Yaa Hayyu Yaa kayyum'. Fatan ta Allah yasa kar wannan lamarin ya zama gaske domin ita kadai ta san tsananin da za ta shiga ta sani Umma Za tayi fushi da ita fushi mai tsanani ita kuwa ba abin da ta tsana a duniyar rayuwarta kamar Umma tayi fushi da ita sosai hakan ke jefa cikin tashin hankali da rashin natsuwa sosai take jin zuciyar da ruhinta na shiga yanayi na matukar ciwo da zafi gami da raɗadi. Nisawa tayi akaro na ba adadi kafun ta sanya haɓar hijabin ta ta goge fuskarta sai da ta natsu sosai da sosai bayan ta kirayi sunayen Allah a zuciyar hakan ya rage mata faduwar gaba. Da Sallama dauke a bakin ta ta shiga cikin gidan wani wawan faduwar gaba taji ya ziyarce ta zaune ta hango su sun kafa da'ira kamar ko yaushe yarda kasan ƙawaye haka suke daukar junansu sam! Goggo Marka bata rike girman ta ba ta tauna lafazi kafun ta furta a gaban Hafsi bata kunyar ta saki baki tayi ta ratata zance ko wani iri ne ya dace ko bai dace ba ita ba ruwanta. Kasa tayi da kanta tana mai jan numfashi gabanta na cigaba da bugawa fata take yi Allah yasa har ta shige daki ba tare da sun tsinka mata ba domin ta sani in har su kayi magana to ba mai dauke da alheri bane mugun abu za su fadi akan ta ita kuwa ciwon da zuciyarta take yi a yanzu ya isheta ba sai sun dauko wani sun kara mata ba. "Hehehehe an dai ji kunya wallahi an fita da sunan zuwa makaranta ashe halin bera akayi shiyasa ake ta ɓarin jiki a je a turmushe kudin sai gashi da yake Allah ba azzalumin bayin sa ba ne a gaban saurayi ko nace abokin sheke aya asiri ya tonu". Sautin muryar Goggo Marka ta doki kunnuwar Mariya da mugayen kalaman da take furtawa wata irin juwa taji ana yi da ita a filin duniyar rayuwarta ji tayi komai na kwance mata komai take ji ya na fadowa kanta da kayan tashin hankali wani bugu taji zuciyarta tayi kamar zata faso kirji ta fito wani makaƙi mai ɗaci gami da ɓauri taji suna yawatawa cikin makoshinta zuwa saman harshenta. Cak! ta tsaya waje guda tana faman jan numfashi don ji take numfashin na kokarin ficewa gabadaya daga gangar jikinta yake yi a hankali ta fara taka kafafuwanta da take ji suna lauyewa kamar roba suna kokarin watsar da ita. "wai mu za a nuna wa son addini da tsoron Allah bayan ko an fita ba can wajan neman ilmin ake yi ba sa dai yawon ta zubar". muryar Goggo Marka ta sake fadin haka kafun Hafsi ita ma ta caɓe. "rungume da juna fa na tadda su cikin mota yana faman laguda ta ita kuwa sai faman yashe mssa baki take yi". 'A'uzubillahi minal shaiɗanir rajim' Zuciyar Mariya ta shiga ambata tashin hankalin da take ciki ta ji yana daɗuwa komai taji yana juya mata kanta da gangar jikin ta sai majajjawa suke yi da ita cikin wannan yanayi ta ja jiki kanta rike a hannayenta wanda take jin sa kamar zai tarwatse saboda tsabar daukar zafi da taji yayi. Shigar ta dakin ke da wuya ta zube tsakar dakin wani kuka ne mai ɗaci a zuciya taji ya kufce mata sai dai ba hawaye kukan zuciya ne kawai wanda ke kokarin yayyaga mata ko wani fili da zuciyarta da kirjinta HAWAYEN ZUCIYA da take jin suna zuba kamar za su kashe mata zuciya da ruhi. Girgiza kai kawai take faman yi jin lamarin take kamar ba gaske ba jin komai take kamar a duniyar mafarkinta jin komai take yi kamar duk kuncin duniya akanta a sauke mata a duk sassan jikinta wani fili taji a zuciyarta yana kamawa da wuta ya na babbakewa lokaci guda. Lokaci mai girma ta shafe cikin wannan yanayin kafun zuciyarta ta sarara mata dalilin ambaton sunan Allah da take faman yi cikin wani irin yanayi mai girma da tashin hankali a cikin sa sosai idanuwanta suka sauya kala kamar wacce akayi wa hayaki da barkono mai tsananin zafi. A hankali ta dago kanta tana yawatawa da idanuwanta cikin dakin gabanta na tsananta faduwa sake ware idanu tayi ganin ba Umma a cikin dakin da sauri ta zabura ta mike tana kara buɗe idanuwanta sosai kafun ta furta 'Yaa Rabbi'. Laɓɓanta na rawa cikin yanayi na firgata ganin Umma bata cikin dakin hakan ba karamin fadar mata da gaba yayi ba da sauri ta yo waje tana yawatawa da idanuwanta tsakar gidan ba ta ga kowa ba da sauri tayi hanyar bandakin su mai dauke da langa-langa ta shiga kwalawa Umma kira amma ina babu ita babu dalilinta hakan ya sanyata sauri karawasa cikin bandakin ba kowa a ciki da sauri ta yo waje tana duban su Hafsi so take yi ta tambaye su amma tana tsoro ta san dole sun fadi kalma mara dadi ko da kuwa za su bata amsar in da Ummanta tayi ita dai ta san Ummanta ba ma'abociya fita ba ce domin za ta iya tunawa tun da suƙa dawo daga asibiti tsayin wannan lokaci Umma ko kofar gida ba ta leka ba dole hankalin ta ya tashi tana tsoron Abin da zai je ya dawo. Zuciyarta taji tana sanar da ita kawai ta tambayesu kar ta tsorata da abin da za su ce da ita wanda zai bata mata rai domin ko mai su kayi mata baya yake da ace bata ga Umma ba da wannan shawarar tayi amfani ta dago rinannun idanuwanta ta na saukewa akan su kafun ta shiga motsa laɓɓanta gabanta na wani iri bugu mai girma gareta. "Uhmm...Goggo don Allah Umma ta ina ta je...?". Muryarta da rawa a ciki duk kalmar da za ta fadi a dandatse take ajje ta. Duban shekeke sukayi mata su duka kafun Hafsi ta saki shewa suna tafawa tare da Goggo Marka. "mu kika ba ajjiyar ta da za ki zo kina tambayar mu ki fita mana ai gari da yawa maye baya cin kan sa itama ta fice yawon ta kamar yarda ke ma ki fic...". "Hafsi!!!". Mariya ta buɗe muryarta sosai ta ambaci sunan da wani irin bacin rai mai girma dubanta take cikin yanayi na gargaɗi da karki sake tafka irin wannan kuskuren sosai bacin rai ya wadatu a cikin muryarta hannu ta daga tana nuna Hafsi wacce muryar Mariya ita ce ta sanya ta tsaida da maganar take yi domin sosai taji faduwar gaba ganin yanayin da Mariya ta nuna. "Hafsi ya kamata ki san irin maganganun da za ki dinga fadi a kan Umma ta komai za kiyi ko wani irin cin kashi zaki yi ya kamata ki sauke a kaina ba wai sai kin sako Umma ta ba". Ta karashe da gargaɗi mai girma muryarta. Tana gama fadin haka tayi hanyar waje cikin yanayi da zafin zuciya da raɗaɗi a kasan ruhi. Duk kan su sakin baki sukayi suna duban juna kafun Goggo tayi kwaɓa tana girgiza kai gami da cizon yatsa. "ji tsinanniya mai kalar muciya da zani aiko zata ci dangin uwarta bari ta dawo ita da uwar ta ta mai shegen kalan dangin tsiya da shisshigi gami da kwala kai a faranti in ban da haka uban meye hadinta da gidan kultum daga 'yarta ta haihuwa shine ta kwashi jiki zuwa barka za su zo su tadda ni sai sun ga ne shayi ruwa ne ba komai ba ". ******* "Alkawari nayi maka Alhaji Abdulwahaab don haka ka saka zuciyarka cikin ruwan sanyi kamar kayi amarya ta mutu A DAREN FARKO". Areefa ta karashe tana mai kai glass cup da ke zaune a tsakar hannunta mai dauke da tataccen lemon kankana da ya sha kayan hadi sai tashin kamshi yake yi da rangwamin sanyi idanuwanta take juyawa akan Alhaji Abdulwahaab dake zaune yana dubanta da wani irin yanayi mai girma kafun ya saki wani shu'umin murmushi yana gyaɗa kai bayan ya kurbi lemon da ke hannunsa. "Ba ki da dama Areefa. Na sani za ki iya yin koma me nene don ganin cin ma burin ki dama nawa amma kuma ya kamata ki sani Dr.Erena ba saukin kamuwa yake a hannu ba ya kama ta ki san wannan karki yi saurin sakin jiki dashi domin ba karamin NAMIJIN DUNIYA bane da kike ganin sa nan ba ko wacce mace ba ne take samun abin da take so game dashi ya san hannunsa sosai da sosai don haka sai kin yi shiri sosai kafun ki aikata komai karki ga lokaci guda yana rawar jiki akan ki kiyi zaton tarkon ki ya kama miki giwa to wallahi a,a ni nasan halin sa ni zan fada miki waye Dr.Erena ni zan fada miki irin shu'umancin sa". Murmushi a fuskarta take kallon sa dashi sosai take raina maganar ta sa a ranta har yanzu ta lura bai san wacece Areefa ba bai san salon hannnun na taba zata ba shi mamaki za ta nuna masa sabon jini da tsohon jini akwai bambanci a tsakanin su ba kadan ba za ta nuna masa zamanin Dr.Erena gaf! yake da shuɗewa ko ma tace ya shuɗe yanzu kuwa zamanin ta ne ita ce dashi dole kuma tayi amfani da damar ta sannan kuma ta nuna wa Dr.Erena har da shi Alhaji Abdulwahaab din wacece mace za ta nuna masa zamanin da Dr.Erena yayi rayuwarsa bai samu mata irinta ba a duniyar rayuwar tasa dole duk su biyun ta ba su mamaki za su san wacece Areefa. "Ban san da me zan sanar da kai wacece ni ba amma dai zan barka da lokaci shine zai mana Alkalanci a tsakanin ni da kai kawai kai dai ka zuba ido kayi kallon wannan GAME din da za a buga". Ta karashe tana kara sakin wani shu'umin murmushi wanda daka kalle shi zaka san akwai tarko mai girma da aka ɗana cikin sa kafun a sake shi. Gyaɗa kai yake yi yana yawatawa idanuwansa a nata ba tare da fargaban komai ba sosai da sosai ya hango tsantsar rashin tsoro ko SHAKKA cikin idanuwanta sosai da sosai ya hango gaskiyar kalaman da suke fitowa daga bakinta amma duk da hakan bai gasgata ba domin shi ya san Dr.Erena kuma ya san wanene shi a cikin wannan harkar dole Areefa tayi taka tsantsan domin wannan wasan da take ganin shan ruwa ya fishi wahala to tabbas zai iya juyewa a ko wacce dakika ba tare da ta fargaba ya zame mata katon aiki mafi girma da wahala a filin rayuwarta. "Ba wai ina raina yanayin ki ba ne a,a ko daya ina dai so na sanar dake wanene Dr.Erena...". "Ya isa haka!". Areefa tayi saurin tare shi cikin kakkausar muryar kafun ta mike kan kafafunta ta fara taku a hankali tana mai gyaɗa kan ta juyowa tayi a hankali ta dube shi bayan ta tsaya cak! da takun da take yi. "Me yasa zakayi mani haka mai yasa ba zaka barni na karanci wanene Dr.Erena AKARAN KAINA ba mai yasa kake son ka cusawa zuciyata shakka ko wani fargaba akan sa bana zaton wannan zuzutawa da kambawa da kake yi masa zai samu muhalli a zuciya ta ba na tunanin yarda zuciyarka ke shakka a kan sa nima ta wa za tayi haka zuciya ta da taka suna da bambanci sosai da sosai don haka ka kula". Ajje Cup din da ke hannun ta tayi kan table din dake gaban su ta sanya hannu ta dauki jakar ta da mukullin motarta bayan ta watsa masa wani kallo na gargaɗi ta fara taka kafafuwanta domin fita daga cikin Office din ranta a jagule domin kuwa sosai taji raini a maganar Alhaji Abdulwahaab sosai ta hango ya raina ta ya raina yanayin ta amma ba komi zata ba shi mamaki wanda zai jima yana taba masa zuciya da ruhi. "Areefa!". Ya fadi yana mikewa kan kafafuwansa a hankali ya fara takawa domin isa wajanta tsaye take rike da Handle din kofar tana faman jujjuyashi. "Ban san mai yasa kika fiye daukar zafi akan abin da bai taka kara ya karya ba, Ban san wacce irin zuciya gareshi ki wacce take saurin daukar abu da girma ko da kuwa bai kai a dauke shi din ba". A hankali ta juyo tana sauke idanuwanta cikin nashi kafun taja numfashi tana gyara zaman glass din da ta daura a fuskarta a wannan lokaci mai taken 'No respect' wanda yayi matukar karawa fuskar ta ta kwarjini da kyau sosai. "A rayuwa na tsani a raina kwazo na ko ya ya ne shiyasa nake so mutum ya rike duk wasu kalaman sa akai na har ya ga in da zan tsaya da kwazon nawa sai ya bashi Mark daidai dashi". Yanayin da take ajje kalamanta da dakewa a ciki ya sanya shi kara gasgata ta akan kwazon nata da take kambawa amma kuma ba wai fadi a baki ba a,a gani a aika ce shine sahihin aiki inji kare yace 'mu gani a kasa' ana biki a gidan su. Shirun da taji yayi ne ba tare da ya ce komai ba ya sanya ta nisawa domin har yanzu ta lura akwai kokwanto a zuciyarsa murmushi tayi kafun ta juya tana murɗa Handle din tana fadin. "Uhmmm...kar fa ka saka zuciyarka cikin tunanin lamari na kawai ajje shi gefe ka yi kallo kawai kamar yarda na fadi maka a baya". Tana gama fadin haka ta sake sakar masa murmushi tana ficewa daga Office din da hanzari. Sosai yake murmushi shima yana kallon yanayin Areefa da yanayin da take kokarin ya yarda da maganarta zai iya yarda sai sai wani sashi na zuciyarsa yana tuno masa da Dr.Erena yana hango wanene shi a duniyar filin rayuwarsa da irin gamzuwa da yake yi da mutane yana zubda su sosai yake samun nasara kafun a samu kan sa wanda ya tabbatar wannan a jinin sa yake. Juyawa yayi ya koma tsakar Office din yana safah da marwa hannayensa harɗe a bayan sa. ***** April 2000. Sosai garin ya haɗe da wani irin haɗari mai matukar razanar wa wanda a ko wani lokaci zai iya zubda ruwa mai karfi gaske gami da iska. Dr.Erena tsaye bakin kofar dakin wani hotel dake tsakanin Abuja da Suleja kallo daya zaka yi masa ka tabbatar da akwai abin da ke damun sa a ransa sosai da sosai bi sa yanayin da fuskarsa ta nuna na tsananin bacin rai. "Mr. Ekele na lura har yanzu ba ka san wanene ni ba a fadin duniyar nan har kake tunanin yaudarata ka hada baki da wasu wajan cuta ta". Wani murmushi ya ajje a fuskarsa yana kai hannunsa zuwa haɓarsa dake cike da suma kamar wanda yayi shekara ashirin bai bi ta kan ta ba. Mr.Ekele da ke tsaye sai faman rarraba idanuwansa yake yi a tsakanin na Dr.Erena ya shiga sharce gumin da ke tsatsafo masa a ko ina na kofar gashin dake jikin sa na fuskarsa yake saukewa duk da iskar ake yi a wannan lokacin bakin sa na rawa cikin gurbatacciyar hausar sa ya shiga magana. "aleji ke yi hakuri don Allah hakan ba zai sake faruwa ba na rantse miki". Wani wawan kallo Dr.Erena ya watsa masa kafun ya dungule hannu kamar zai sakar masa naushi a fuska hakan da Mr.Ekele ya gani ya sanya shi ja da baya yana kiran. 'Jesus'. Bakin sa na ɓari jikin sa sai karkarwa yake yi kamar wanda aka jonawa wayar wuta. "Get out now!". Muryar Dr.Erena ta karaɗe wajan da amo mai zurfi da bacin rai a cikinsa. wata irin zabura yayi har yana kokarin haduwa da bango da sauri ya juya duk da hakan bai hanashi haɗe hannayensa waje daya yana bashi hakuri ba cikin tsananin tashin hankali. Fitar Mr. Ekele ke da wuya Dr.Erena ya juya cikin dakin sa da sauri fuskarsa kunshe da bakin ciki da bacin rai mai tsanani ga kuma wani murmushi da ya dauko yake ajje a fuskar tashi gefen gadon ya zauna yana mai janyo na'urar sadarwa ta waccan zamanin talfon a hankali ya ja abin sanya wa a kunne ya na mai kai dayan hannun nasa zuwa madannan jikin talfon din dakikun kadan a ka daga cikin yanayi na umarni da nuna isa akan wanda ake waya dashi ya fara magana. "Yanzu nan nake so ku isa titin da zai shigar da ku Abuja Mr.Ekele nan akan hanya ina so cikin mintina goma ya bar filin duniyar nan bana so ko gawarsa a gani balle a shaida shi da cewa ya bar duniyar nan". Yana gama fadin haka kamar da minti daya ya sauke wayar yana faman sakin wani murmushi mai razanar da wanda ya gani kafun ya saki wata mahaukaciyar dariya yana mai bajewa gabadaya kan gadon. Gudu yake yi cikin motarsa zuciyarsa sai faman tsalle-tsalle take da tashin hankali mai girma a wannan lokacin kuma a ka saki wani ruwa mai karfi da iska ga tsawa da ake ta kwaɗawa gabadaya Mr.Ekele ya gama tafiya cikin duniyar tashin hankali jikin sa faman karkawa yake yi ga wani gumi dake karyo masa duk da feshin ruwan da dake shigowa ta cikin glass din motar da bai rufe duka ba. Zuciyarta ba abin da take zaryar dauko masa sai a rangamar su da Dr.Erena ya sani sosai zai shiga cikin matsala tun da har ya san da hannunsa cikin wannan yaudarar da aka shirya yi masa duk da dai shi akaran kan sa ba a son ran sa wannan lamarin ya afku ba takura masa akayi ba yarda ya iya ga shi yanzu ya shiga hali wanda Allah kadai ne zai iya fiddo shi daga hannun wannan mutumin mara imani da tausayin a zuciyarsa ya sani sai wani ikon Allah zai bar shi ya cigaba da rayuwa a duniyar nan ya sani koma ya cigaba da rayuwa to lokaci kalilan ne zai yi ko da kuwa be bar duniyar ba to tabbas zai shiga halin ƙaƙani kayi... Wani iri bugu yaji an yiwa bayan motarsa wanda sanadiyyar haka sai da ta tuntsiya ta shiga katantanwa a tsakiyar titi ga ruwa da ake ta mamakawa dakiku masu yawa ta dauka tana katantanwa kafun ta tsaya waje guda bayan ta dawo daidai gabadaya glass din jikin motar su yi kwatsa-kwatsa ita kanta motar duk ta gama molewa Mr.Ekele da ya gama rikicewa gabadaya kansa da fuskarsa jini ne sosai gabansa sai bugawa yake yi da sauri sauri a hankali ya fara kokarin tayar da motar don ya gama tabbatar wa kansa ba wanda zai yi masa wannan aikin sai Dr.Erena tuni ya tabbatar wa kan sa ba zai bar shi da numfashi a doron duniyar nan ba key ya shiga juya a mazauninsa cikin iko na Allah motar ta dau wuta ganin ta tashi yayi mata birki gami da fizgarta kamar daga sama yana yin gaba yaji ya doku da katon abu wanda ya sanya motar sake wuntsulawa baya can bayar ma karo ya sake yi da wani abu mai girman gaske kafun motar tayi sama ta dawo kasa lokaci guda. Izuwa wannan lokaci ya gama fita daga hayyacin sa ba abin da yake ambata sai 'jesus' ya ce ce shi daga wannan halin da yake ciki na tashin hankali. A hankali yaji a na bugun motar tasa kamar daga sama lokaci guda ya ji an balle murfin wani irin haske ya ga an dalle masa idanuwa dashi wanda hakan ya karasa rufe masa ganin nasa da jini ya wanzu a fuskar sa gabansa ne ya cigaba da faduwa yana ji ya na gani aka fizgo shi waje aka watsar tsakiyar titi kamar wani kayan wanki sosai ya bugu a bayansa wanda hakan ya sanya shi sakin kara mai sauti bai kai ga dire karar ta sa ba yaji an kwaɗa masa wani abu mai girma a tsakar kai wanda hakan ya kara sanya shi bajewa a tsakiyar titi yana mai sakin numfashi wahalalle wata tsawa kayi mai dan karan haske hakan ya baiwa Mr.Ekele damar ganin mutanan dake tsaye akansa gabza gabza har su biyar ko wanne rike da mugun makami a hannunsa hakan ya kara tsinkar masa da gaba ya sadakar shi tashi ta kare a filin duniyar nan a hankali ya mai da kansa ya langwaɓar jira kawai yake yi yaji saukar wani makamin wanda zai tafi masa da rai daga gangar jikinsa. "Kai dan uban baban ka shine don ka raina wa oga sense shine zakayi masa eya ne ko to yau zaka bar duniyar nan dan kundun uba jikan oduduwa mai katon ciki". muryar dake wannan zantukar kadai in ka saurara zaka gane tsantsar rashin imani da tausayi daga ji kuma zaka gane ma'aboci zuke-zuke ne zauna gari banza da ake amfani da su wajan cutar da jama'a da ba su ji ba su gani ba. "Bobby kawai yi masa eya ne kamar yarda ya yi wa Oga shi ya yaji inda dadi". Wata muryar ce ta daban ta sake fadin haka. A wahale Mr.Ekele ya motsa yana mai sakin numfashi mai tsananin ciwo. "ki taimake ni kin ji karki kashe ni zan baki duk abin da kike so Allah...". Wani bugun bazata yaji ya saukar masa a baki wanda ya sanya shi zubewa a kasa yana kiran jesus ya cece shi za su kashe shi. Wata irin shaka ya ji anyi wa wuyansa kafun lokaci guda a durkusar dashi a dage masa kai yana ji yana gani aka daura masa wata irin sharɓebiyar wuka wanda walwalin ta ke haske duhun daren da suke ciki kafun yayi wani yinkuri tuni an sauke kan sa a kasa yabi titi yana ta tintsirawa yana tsartuwar jini gangar jikin kuwa nan suka yi cilli da ita kafun daga bisa suka dauke ta sukayi cikin motar shi da ita suka banka masa wuta lokaci daya kamar an kunna wutar auduga haka ta kama ranga ranga. A hankali suka shiga motocin su fuskar su na bayyanar da tsantsar murna da farincikin samun damar cika wannan aikin domin sun tabbata da ba su samu wannar sa'ar ba Allah kadai ya san abin da Dr.Erena zai musu domin sun lura sosai Mr.Ekele ya bata masa rai wanda ya kasa boyewa har sai da ya fiddo a muryarsa suka fahimta kuma yayi musu gargaɗin kar su sake a samu akasi akan aikin nan sannan ga kudin da ya saka musu masu auki wanda tun da suke yi masa aiki bai taba basu kudi haka ba. ***** "Yaa Allah! Dr.Erena kasan me ke faruwa kuwa yanzun nan muna kan hanyarmu ta dawo wa daga Abuja mu kayi kaci ɓus da wani abun tashin hankali Mutumin ka Mr.Ekele an kashe shi an kona gawarsa har da motarsa sai dai kuma kansa da aka yanke kafun a ko ne shi shine yasa muka gane shi ne". Numfashi mai karfi yaja kafun ya saki Murmushi mai cike da mugunta har sai da Alhaji Abdulwahaab yaji sautin. "Ni na sanya aka kashe shi?". "What! kai fa kace akan mi?". "wannan ba damuwar ka bace abin da kake bukata na fadi maka don haka ka rabu dani kawai a wuce wajan domin ni har na manta da wani mai irin wannan sunan a filin duniyar nan". "Yaa Salam! Me ya sa kayi haka Dr.Karami haka sam bai dace ba Mr.Ekele komai yayi maka bai dace ace ka sanya anyi masa wannan mugun aikin b...". "Ya kamata ka kiyaye lafazun ka Alhaji Abdulwahaab na rantse da Allah ko kai ne kayi mani abin da Waccen mataccen yayi mani sai na sanya a kau da min da kai a filin duniyar nan wallahi don haka ka kiyaye lafazinka". "Dr.Erena ni ka ke wa ikirari haka Allah ya baka hakuri ban san lamarin zai taba maka zuciya har haka ba". "Da dai yafi haka wallahi don haka mu yi wani batun na daban in kana dashi in kuma babu mu sauke wayar". Murmushi Alhaji Abdulwahaab ya saki mai zafin gaske kafun ya nisa. "Ni ba ni da wani abin cewa dama akan waccan maganar ce kuma kace ba ka so komai ya wuce". Bai jira cewarsa ba ya sauke wayar yana mai mamakin Dr.Erena da irin rayuwar da yake yi wa kansa tanaji ko da yake bai kamata ya zauna tunanin sa har haka ba tun da shi ma akwai tasu a tsakaninsu.... Nisawa Alhaji Abdulwahaab ya yi sosai lokaci guda gumi ya karyo masa duk da sanyin A-c dake busawa cikin Office din tausayin Areefa yake yi akan yarda lokaci guda ta daukar wa kanta wannan aikin mai cike da hatsari da tarin kalubale shi kansa tsoron Dr.Erena yake yi kuma yana tsoron ranar da zai san yana bibiyarsa ya san tabbas shima wani abu zai faru dashi sai dai zai wa kansa Alkawarin ajje duk wani fargaba da tsoro akan Dr.Erena ya fuskance shi ya marawa Areefa baya domin ganin sun cin ma abin da suke bukata akan sa sosai yake jin zafi da raɗaɗi a zuciyarsa duk lokacin da ya tuno da kunci da bakin cikin da Dr.Erena ya cusa masa a zuciya dama filin duniyar rayuwarsa gabadaya. *KAMALA MINNA*😘😘 [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA ASHIRIN DA UKU. Sosai take jin maganganun Alhaji Abdulwahaab na mata kuwwa a kunne ta rasa mai yasa haka, ta rasa mai yasa zuciyarta take koƙarin dauko mata abin da bata shirya tarbarsa ba, kokari take ta kau da komai a zuciyarta wanda sam bata muradin ace sun shigo har suna ƙoƙarin sanyata wani hali Dr.Erena mutum ne da ya kama ace ta ajje komai nata ta fuskance shi sosai da sosai sannan duk wata fargaba ko SHAKKA gami da tsoro ya dace ma ace babu su a filin rayuwarta. Nisawa tayi tana mai jan numfashi mai zafi tana fesawar wasu lamura ne masu matukar tasiri a rayuwarta taji suna dawo mata kamar yanzu ne suke fado duniyarta ji take yi kamar yanzu ƙaddara ta hadata da Dr.Erena komai taji ya sanko mata lokaci guda a zuciyart da sauri ta ja burki a gefen titi tana mai hada kanta da sitiyari zuciyarta taji tana wani lugudan bugu wasu hawaye masu tsananin zafi da kokarin yayyaga zuciya suka shiga zubo mata... ******* *JANUARY 2004.* *KADUNA GIDAN MARAYU.* "Alhaji Mati ba wai ban yarda da kai ba ne, kawai dai ka san sha'ani na rayuwar a wannan zamanin sosai yara irin wadannan suke shiga kuncin rayuwa a hannun wanda suke daukar su anyi ba sau daya ba, ba sau biyu ba a nan gidan shiyasa kaga gabadaya yanzu ba ma yarda da mutane sam! da suke zuwa daukar marayu da sunan rike su wasun su da yawa ba saboda Allah suke daukar su ba su da tasu manufar akan marayun da suka dauka...". Nisawa yayi yana kara gyara glass din fuskarsa kafun ya dubi Alhaji Mati da yayi masa kuri da idanu yana dubansa kamar zai cinye shi danye sosai yake jin zafi da raɗaɗi a zuciyarsa sosai da sosai yake jin zuciyarsa na wani irin zugi ji yake yi kamar ya tashi ya makure wannan mutumin da yake kokarin yi masa sakiyar da ba ruwa ba zai yarda ba da wannan gangancin ba ba zai lamunci wannan haukar da wannan mutumin ke kokarin yi masa ba. Nisawa yayi yana kokarin boye bacin ran dake kokarin bayyana kansa a fuskarsa wani shu'umin murmushi ya kalato ya sauke kafun ya kau da kai yana hirji kasa-kasa. "a zamanin nan da muke ciki da yawa marayun da ake dauka suke shiga gararin rayuwa suke shiga tashin hankali sai mutane su zo da sunan ba su da 'ya'ya Allah bai basu haihuwa ba a taimaka a ba su za su rike tamkar 'ya'yan cikin su amma daga baya bayan sun samu cikar burin su sai su canza alkibla akan 'ya'yan da aka ba su da KUDIRI da sukayi niyya a zuciyarsu ba zan boye maka ba Alhaji Mati ka ganni nan nayi kuka da idona da girmana da kake gani a haka akan tashi hankalin da marayu suke shiga a hannun masu daukar su da sunan riko ban san adadin yawan marayun da suka bata ba ban san adadin marayun da aka bata wa rayuwa ba ban san adadin marayun da aka ciwa zarafi ba ban san adadin marayu mata da aka KETA HADDI a garesu ba haka ma mazan su ma ba a bar su ba...". Shiru yayi yana jan numfashi zuciyar na wani irin bugawa ransa na kara ɓaci a hankali ya ja glass din idanunsa ya dauke wasu kwalla da suka tarun masa kafun ya sake nisawa yana duban Alhaji Mati da izuwa wannan lokaci ya kosa da dogon sharrin da yake yi masa wanda shi dai a karan kansa ba abin da suke yi masa domin bi sukeyi ta bayan kunnan sa suna wuce wa ba abin da ya kawo shi kenan a zaunar dashi ana karanta masa halin marayu ba shi zuwa yayi a bashi abin da yake bukata ko nawa ne zai biya a zuciyarsa ba wai marayu ya zo dauka ba siyar maraya ya zo yi da kudin sa domin bukatarsa ce ta taso a filin duniyar rayuwarsa. "MARAYU MA 'YA'YA kamar ko wani ɗa a filin duniyar nan suna da gata da galihu gami da 'yanci a rayuwarsu kawai dai har yanzu ba a san wanene maraya ba duk marayu da ka ga ana ajje su a wannan gidan to in ka bincika ba su da laifin ko miskala zarratin a filin duniyar su da yawan su haihuwar su ake ana yasar da su a titi ba tare da sun sani ba da yawan su iyayen su da suka haife su ba wai ta hanyar sunna bace ake samun su ya kamata a daina ganin laifin marayu ba su suka halicci kan su ba haka ƙaddarar su ce ta zo a hakan in da suna da iko wallahi ba yarda za ayi su bar iyayensu su haife su ta wannan gurbatacciyar hanyar...abin takaici yawan mutanan mu ba sa duba ga hakan kawai yankewa maraya hukunci suke yi da bahagon tunani ya kamata ace an daina ganin laifin maraya maraya rauni gareshi maraya mai bukata ne a filin duniyarsa maraya shima ɗa ne kamar ko wani ɗa a filin duniyar nan...". Nisawa yayi muryarsa a lokacin ta kara rauni. "...don Allah Alhaji Mati ka dubi girman Allah da Annabi kayi mani alkawari ba zaka zamo daya daga cikin mutane da masu cin zarafin marayu ba...". "Ba sai ka roke ni ba Uban Marayu". Alhaji Mati ya fadi da murmushi kwance a fuskarsa kafun ya cigaba da cewa. "Bana cikin irin wadannan mutanan masu tauye hakki har haka ka yarda dani Alkawari nayi maka ba zaka samu matsala dani ba domin nasan darajar maraya domin nima na ɗanɗani irin rayuwar tasa kuma ban ji dadi ba ka ga kuwa ba yarda za ayi ace na so wani dan uwa nawa ya shiga irin wannan halin". Ya karashe da yanayin rauni a fuskarsa. "Naji dadin haka sosai da sosai Allah yayi mana jagora". Bai amsa ba illa yatsine fuska da yayi cikin yanayi kamar akwai abin da ke damun sa yana mai duban yarinyar dake zaune can gefe da su ta takure waje daya a shekarun ta ba za su hau goma zuwa sha daya ba fara ce tas! kamar shuwa bata da jiki sosai kallo daya zakayi mata ka gane irin matan nan ne ma su tsayi da kirar jiki. Duban ta sosai Alhaji Mati yayi zuciyarsa na wani irin zullon farin ciki KUDIRI da burinsa gaf! suke da cika komai na duniyarsa ya kusan zamar masa sabo filin a leda. Takardun da yaji Uban Marayu ya turo masa gabansa ne ya tsinke masa tunanin da yake yi cikin yanayi na son abin da aka turo masa ya dauki takardun yana yawatawa da idanuwansa kan su yana mai sakin wani Shu'umin murmushi. Takardu ne na yarjejiniyar da sukayi a tsakaninsu zuwan sa na farko da suka je kotu komai da komai gashi nan a rubuce har da sanya hannun lauya da shi uban marayun. Duban sa yayi kafun ya numfasa. "Uban marayu na ga komai kuma hakan yayi daidai sosai da sosai" ya fadi yana mai dauko Biro yana sanya hannu a wajan da Uban Marayun ya nuna masa da hannunsa. "Godiya muke sosai Uban Marayu". Alhaji Mati ya sake fadi yaka mai mika masa hannu suna gaisawa duk kan su da murmushi a saman fuskarsu. Matar da take gefen sa zaune ya duba yana murmushi. "Hajiya kiyi masa godiya ta tabbata yau dai mun samu 'ya". Tsukankiyar matar mai kama da muciya da zani fuskar nan ta ta tasha mai sai kyalli take da wani kala-kala kallo daya zakayi mata ka kau da kan ka. Yak'e ta saki tana mai washe hakoranta da suka gama dafewa da dattin hayakin sigari godiya tayi kamar bata so ba kafun ta mike tana sabar jakarta. Dama tuntuni sunyi komai da komai jira kawai suke su samu damar tafiya daga wajan Uban Marayu. "Khairiyya shikenan kuma kin bar mu kin ga yanzu ga iyayenki nan da za ki koma wajan su da zama ina yi miki fatan alheri a rayuwa". Khairiyya dake kwakumi da jikinta da sauri ta dago idanunta da suka ci taf! da hawaye tana dubansa sosai yaji ta bashi tausayi a ransa kau da kai yayi don ya san tabbas in ya cigaba da kallon ta shima hawaye zai yi gaban sa yake ji yana bugawa amma bai kawo komai a kai ba kawai tunanin sa kamar yarda ya saba rabuwa da marayu cikin damuwa yau ma haka ne yake ji dalilin rabuwa da Khairiyya. Kuka sosai take yi har suka fito daga cikin gidan bayan sun yi BANKWANA da yan uwanta sai kuka suke yi suma tana ji tana ga aka sakata cikin motar Alhaji Mati cikin yan mintina kalilan suka bar harabar gidan kallon gidan take yi tana ji a ranta ba za ta sake dawowa ba kallon gidan take yi kallo na karshe a filin rayuwarta tana ji a ranta bazata sake zuwa cikin gidan nan ba in ba wani iko na Allah ba sosai take ji gabanta na faduwa duk lokacin da ta kalli Alhaji Mati ko kuma taji amon muryarsa mai razana ta. Tafiya mai nisa sukayi tun tana hango gidaje har suka fara shiga dazuka masu bishiyoyi kala daban-daban izuwa nan lokaci ta tsaigaita da kukan da take sai jan numfashi take tana ajiyar zuciya. Awanni Hudu sukayi a hanya kafun su iso cikin Garin Sulaje suna kokarin shiga cikin gari Alhaji Mati yayi parking gefen titi yana duban matar dake gefensa zaune murmushi yake saki mai dauke da mugunta a ciki. "kin gama aikin ki don haka ga tukuicin ki". Ya fadi yana sanya hannu cikin aljihunsa yana zaro bandir din yan dubu dubu guda biyu ansa tayi tana mai kau da fuska kamar bata so ba. "Sannan kuma wannan lamarin ya kasance tsakanina da ke in har naji labari mai kama da shigen wannan lamarin kin san Allah sai kin bar filin duniyar nan". Ya karashe fuskarsa a daure kamar bakin hadarin dake kokarin zubda ruwa. Ko a jikin ta bata nuna damuwa da maganganunsa ba illa tsaki da tayi can kasar makoshi ta na balle murfin motar ta fice Khairiyya dake takure bayan mota ta duba da wani irin yanayi na tausayawa tana faman gyaɗa kai kafun ta dubi Alhaji Mati. "batar da sunanka sananne ka aro na banza ka sakawa kan ka akan wani KUDIRI naka na daban...Uhmm ba na ganin wanda ya isa rikakken mutum mara tsoro zai fito da wannan salon na boye sunan sa domin duk wanda yake so ya fado DUNIYAR SHAHARA a wani fanni da sunan sa ya kamata a san shi ko an rufe babin sa ba za taba mantawa dashi ba da abin da ya aikata". Tana gama fadin haka ta buga murfin motar da karfi yan yatsunta biyu ta dagawa Khairiyya wacce a wannan lokacin ta dago da kanta tana dubansu su duka biyun cikin yanayin na rashin inda suka dosa a tsakanin su. "Hajiya Layla" Ya fadi da murmushin mugunta a laɓɓansa kafun ya dora. "...abu daya zai sa na kyale ki a filin duniyar nan shi ne wannan yarinyar da kika bada takomashin taimako har na same ta saboda ita ce hanyar samun arzikina da nake burin cimma wa wannan dalilin zai hanani yi miki komai amma duk da haka ki tsumaye ni ina nan tafe". yatsine fuska tayi kafun ta juya ta fara takawa kan kafafuwanta. Dariya yake yi sosai da sosai har yana buga sitiyarin motar kafun ya tsagaita kamar daukewar ruwan sama fuskar nan tashi ya haɗe ta waje daya kafun yayi wa motar ki ya fizge ta kamar mai kokarin tashi sama. tafiya yayi mai dan tsayi mai makon ya shiga gari kawai sai ya ratse ya yanki daji hakan da Khairiyya ta gani ya dan tsoro ta ta ware idanu tayi tana duban hanyar da suke shiga daji sosai da sosai tun suna hango gidaje har suka daina sai bishiyoyi kala kala can nesa kadan ta hango wani gida shi kadai kwallin kwal! a tsakar daji ba ka jin kukan komai sai na tsintsaye da sauran halittun daji gida dan madaidaici ne anyi masa farin fenti gabadayansa haka kwanon rufin ma fari ne aka saka. A hankali Alhaji Mati ya isa kofar gidan yayi Parking ita dai Khairiyya gabanta sai faduwa yake yi ta saki baki tana kallon gidan tana jin sa lokacin da ya buɗe kofar ya fita kafun taji amon muryarsa akanta a dan razane ta dube shi kafun tayi kasa da kai gabanta na tsanan ta faduwa a hankali ta fara kokarin fito bayan ya bude mata kofa ya turke a gefe gyara zaman babbar rigarsa yake yi kamar wani sabon ango gefen sa ta ratsa ta tsaya hannunta harɗe waje guda a kirjinta. "Muje ko". Ya fadi yana kamo hannunta wani irin razana tayi idanuwanta sukayo waje gabadaya jikinta ya shiga rawa kamar wacce wayar wuta ta kama. Bai damu da yanayin da ya ga ta shiga ba haka ya ja ta har zuwa kofar gidan ba tare da wani shamaki ba ya turo kofar ya shiga ba kowa a tsakar gidan sai fili kawai da aka malale da sumunti kallo daya zakayi wa gidan ka gane ya na samun gyara sosai da sosai duk girma gidan da fadinsa daki daya ne jal! sai can gefe kuma wani dan karamin daki ne wanda kallo daya zakayi masa ka gane makewayi ne. "Dr.Erena da kan sa". Kamar daga sama suka ji muryar ta amsa amo a filin gidan baki daya da sauri Khairiyya ta shiga dube dube don ganin daga in da muryar take amma bata ga kowa ba tana cikin wannan halin taji Alhaji Mati ya ja hannunta sun nufi dakin nan guda daya ta so ta tirje amma sai ya sa mata karfi ya shigar da ita dakin zaune su ka tadda shi babban mutum ne wanda a kalla zai baiwa shekaru hamsin baya sanye yake da riga da malum-malum farare tas sai rawa ni shima na farin kyalle ne duk dakin haka aka kawata shi da farin abubuwa dangin su kwarya da su casbaha da sauran su gabansa kuma in da yake zaune wani faskeken faranti ne shima fari ne an cika shi da yashi mai laushi sosai gefe da gefen faranti din goran duba ne cike da wani farin ruwa mai daukar ido sosai da sosai. "Ita ce wannan?". Mutumin ya fadi yana mai kallon Khairiyya da wata irin siga kafun ya sake duban Alhaji Mati da shima yake ta faman yashe baki burin sa ya kusan cika wannan karon Malamin sa ko mu ce boka bai katse masa hanzari ba. "Irin wadannan ake so masu kyau da tsari sosai wanda kai a karan kanka sai kaji komai daidai amma da kaje kana kwaso yaku bayi ina aiki zai yiwu kasan komai yan son MAI ƘYAU domin har kace za ayi ta arziki da kyau kuma". Shi dai Alhaji Mati sai zabga murmushi yake yi kamar ango a daren farko hankalin sa gabadaya ya koma kan Khairiyya da jikin ta ya fara rawa jin kalaman da suke fadi akan ta ko ba a fadi mata ba tabbas akwai abin da ake kokarin yi akanta. Wani Alkalami ya dauko wanda aka shafe jikinsa gabadaya da farin wani abu amma daga kansa in da aka yi don dangwalo tawada bakinkirin ne sosai. Nuna Khairiyya ya shiga yi da shi kafun ya dubi Alhaji Mati yana mai saka laɓɓansa duka cikin bakinsa yana tsotsawa kamar wanda ya samu alawa. "Zan yi mata wani aiki yanzu ina bukatar kadaicewa ni da ita". Ya fadi da wani murmushi a fuskarsa sosai Alhaji Mati ya shiga gyaɗa kai yana faman sakin yak'e haka da Malamin ya gani ya sanya shi mikewa da wani zabgegen carbi a hannunsa yana mai yawatawa akan Khairiyya kafun lokaci guda ya watsa shi gaban Alhaji Mati. "Zabi guda daya". Ba musu ya kai hannunsa ya sauke kan 'ya'yan carbin ya zabi daya gami da mikawa Malamin ya ansa kafun yayi jim na dan lokaci bakinsa na motsawa sannan ya tofe a jikin zabin Alhaji Mati yan sakanni ya dauka kafun ya dubi Alhaji Mati. "Tun yanzu duniyar nasarorinka sun fara shan sharafin su don haka ka fara lissafin kan ka a cikin manya-manyan ATTAJIRAN DUNIYA". Wani irin murmushi ya kufce masa kafun ya dubi Khairiyya yana jin wani irin nishaɗi da farinciki na ƙaruwa a ko wani fili na zuciyarsa dama duniyarsa baki daya. "Dakyau Malam Dan-Tani". Gyaɗa masa kai yayi yana masa nuni da ido da yayi wa Khairiyya magana ta biyo shi ba musu Alhaji Mati ya dubi Khairiyya da ta gama hargitsewa gabadaya. "Tashi ki bi Malam yayi maganin ganin iyayenki". Wani irin ware idanu tayi tana dubansa kamar ta ga bakuwar fuska a filin duniyarta cikin hanzari ta mike har tana kokarin faduwa hanyar da taga Malam ya nufa nan tabi labulan da ke jikin bango taga ya yaye sai ga wata kofa ta bayyana ba tsoro komi ta bishi bayansa ta shiga. Daki ne dan madaidai ci ba komai a cikin sai buzu babban dake shimfiɗe a tsakar dakin sai wata babbar kwarya wacce aka zane da rubutun sunayen Allah da farin abu shi ba fetti ba sannan shi ba tawada ba. "Cire kayan jikin ki duka". Kamar daga sama taji ya fadi haka a dan razane ta dawo daga tunanin da ta fada ta shiga dubansa da idanuwanta da sukayo warwaje kamar mai son fashe da kuka. "Ki cire kayan ki nace". Ya sake fadi a wannan karo wata murya ce mai sauti yayi maganar da ita hakan ya tsora ta ta sosai da sauri tayi baya tana kokarin ficewa daga dakin kafun ta yi taku biyu ya fizgo ta wata kara ta saki hakan da ya gani da sauri ya janyo wani dan karamin buzu ya yafa mata a fuska gabadaya jikin ta ya saki lokaci guda ta zube kasa kamar matacciya. Cikin hanzari ya dauko wani katon Alkalami ya tsoma cikin katuwar kwaryar nan dake girke tsakar dakin bayan ya fito dashi ya shiga yan tofe-tofe din sa fuskar Khairiyya ya dosa yana wani irin rubutu a jiki shi ba chainanci ba shi ba indiyanci ba sannan shi dai gashi gashi nan za dai a iya dangantashi da na Arabic bisa wasu harufa da suke yawo cikin rubutun da yake mata a fuska. Sai da ya zane ko ina ns fuskarts kafun ya zare dan kwalin dake kanta sosai gashin kanta ya bazu wanda ya kasance mai yawa gashi baki sidik! Sannan ya zare rigar jikinta nan ma zane mata jiki yayi da rubutun kafun ya zare mata dogon wandon dake jikinta da dan kanfai dinta nan ma zane ta yashiga yi ta ko ina har da farjinta.. (Wa'iyazubilla!) sai da ya tabbatar ko ina na jikinta ya samu rubutun da yake yi kafun ya dawon kan gashin ta ya shiga ya mutsawa da ruwan da yayi rubutun sannan ya mai da mata da kayan jikinta sakanni kadan da kammalawar ya dauko buzun nan ya shafa a fuskarta lokaci guda ta dawo hayyacinta da sauri ta mike tana kokarin zurawa da gudu ya sanya hannu ya kamota ya zaunar da ita. "Ba abin da zan miki zauna ki huta yanzu za ku tafi ki ga iyayenki". Ba musu ta koma ta zauna shi kuma ya tashi ya fice wajan Alhaji Mati ya koma kafun ya zauna yana mai jan carbin da ya samu zube. "An kammala komai yanzu aiki ya rage gareka". Gyaɗa kai yayi yana faman murmushi kafun Malamin ya cigaba da cewa. "Aikin da yake gaban ka yanzu shi tun daga daren yau za ka fara amfani da ita wato saduwa har na tsawon kwana uku a ko wani kwana daya kuma sau uku zaka sadu da ita a dare ka ga ya kama sau tara kenan zaka sadu da ita a dare uku daga ranar da ka cika kwana ukun to a ranar zata bar gidan ka karka sake ko minti tara ta kara domin za a iya samun matsala mai girma wanda za ta iya ruguzo aikin mu da muka ɗade muna kokarin cimma sa". Wani irin dokawa gaban Alhaji Mati yayi amma bai bari Malamin ya gane ba ya shiga yaƙe yana sharce gumin da yake ta faman tsantsafo masa duban Malam yayi. "Amma Malam kai fa kace ba zan taba kusantar mace ba Amma kima yanzu...". "Nasan da haka shiyasa nace daga dare na uku karka sake kulata kar ma ka sake ta kwana gidan ka". Hadiye miyau yayi mai tauri jin samun mafita da yayi amma da duk ya gama ruɗewa jin bayanin da Malam din yayi masa. "za ku iya tafiya". Ya fadi ya na kau da kai daga kallon sa. Tashi Alhaji Mati yayi jiki a sanyaye ya kira yi Khiariyya da sauri ta fito tana duban su daya bayan daya. "Zaka ji sako na Malam Dan-Tani nan zuwa gobe". Bai ansa masa ba illa gyaɗa kai da yayi. Hannunta ya ja suka fice bayan yayi masa Sallama. Suna shiga mota ya dau hanya izuwa lokacin dare ya fara shigowa sosai don har an idar da Sallar issha'i. Cikin mintinan da ba su haura talatin ba suka isa wani tankameman gida mai rai da lafiya wanda kallo daya zakayi masa sai kayi zaton ba a filin kasar najeriya yake ba saboda yanayin tsarin gininsa da kayan alatun da aka zuba. Bayan yayi Parking wajan sauran motocin gidan suka fito yana rike da hannun Khairiyya har suka isa kofar da zata sada su da baban falon gidan key ya saka ya buɗe suka shiga. Yaa Allah! Zo ku ga Aljanar duniya tsayawa tsara suffar falon ma katon aiki ne a gare ni ku dai ku baiwa kan ku amsa da kan ku makaranta. Zaunar da iya yayi akan duma duman kujerun Falon kafun ya zare babbar rigarsa ya yasar a nan ya sake cire yar ciki ya sake ajjewa ya shiga kokarin kwance wandon sa da sauri Khairiyya tayi kasa da kai tana dukunkunewa waje daya numfashinta taji yana sama da kasa kamar zai dauke sosai da sosai ta firgita zuciyar tashiga bugu ba ƙaƙƙautawa. Ba ta san lokacin da ya iso gareta har ya zauna ba kawai jin hannun mutum tayi a jikinta da sauri ta kara takurewa kafun ta dago idanuwanta da suka rine lokaci guda. 'Innalillahi wa inna ilair raji'un'. Abin da ta fadi kenan a zuciyarta ganinsa tumbur haihuwar uwarsa komai na halittarsa a bayyane yake ba ta san lokacin da ta saki wata wawuyar kara ba gami da kokarin mikewa amma ina ta kasa domin lokaci guda taji ya daukota gabadayanta ya ajje kan cinyarsa ya shiga yage duk wata suntura dake jikinta fuskarsa dauke da murmushin mugunta wani irin yanayi yake ji a jikinta dama zuciyarsa baki daya ya shiga lumshe idanuwansa bayan ya kammala zare mata komai na jikin ta ta koma haihuwar uwarta ita ma kuka take yi wanda bata san lokacin da ya kufce mata ba sai faman tirje tirje take amma ina hakan bai hanashi haike mata ba cikin yanayi na karfi yake sarrafata kamar zai karyata ita kuwa ihu take yi amma ina ba alamun wani mai cetonta tun tana ihun har muryar ta ta dashe lokacin da ya shigeta tun da ta saki wata kara bata sake sanin in da kanta yake ba har yayi kidin sa yayi rawarsa ya ta shi ya barta nan yashe cikin yanayi na tashin hankali da taba zuciya komai nata in ka kalla sai ka kau da kai domin kace kace yayi mata kamar ba mutum mai rai a jiki ba kujerar da take kai kuwa kamar an yanka kaza a wajan tayi FESHIN JINI haka ya koma. Ba ita ta farka ba sai cikin dare sosai da wata irin kara ta saki ta tashi jikinta na kyarma kuka take yi kuka mai taba zuciya kuka ne take yi wanda ba ta san iya lokacin da zata daina shi ba ko ina na jikinta ciwo yake yi mata ga wani zafi da raɗaɗi da take jin sa ya na amsa wa har cikin kanta tun daga mararta har zuwa kafafuwanta ji take yi kamar ana saka guduma ana kwankwatsa su. Cikin wannan yanayin garin Allah ya waye haka ya fito ya tadda ita ko kallon arzuki bai yi mata ba ya sa kai ya fice bai sake dawowa ba sai dare a wannan daren ma haka ce ta kasance don Khairiyya ji tayi kamar a daren ranar da ya kawota gidan ba komai yayi mata ba don sai da ta gwanma ce da ma ta mutu suma dai bata san iya adadin da tayi ba. A dare na uku kuwa har yayi ya gama bata ta sani ba don gabadaya ba numfashi a jikinta shi kansa sai da yayi tunanin mutuwa tayi yana kammala abin da yake yi ya mai da kayansa ya dauke ta a cikin wannan mugun halin ya saka ta a motarshi yaja ya fice daga cikin layin sosai yayi nisa da unguwarsu kafin ya sami gefen titi ya fito a hankali kamar wanda fitsari ya matsawa zai yi haka ya ja motar sosai gefe yayi Parking ya fito ya buɗe ya zaro ta har zuwa lokacin ba numfashi a jikinta ya yasar da ita sai da ya dubi gabas da yamma kudu da arewa ya ga ba wanda ya gan shi domin lokacin dare yayi sosai da sosai ya ja motarsa yayi gaba zuciyarsa fes! KUDIRI da burinsa sun cika zai zama daya daga cikin ATTAJIRAN DUNIYA. Gudu yake yi sosai fuskarsa na bayyanar da jin dadi har ya koma gida yayi wanka ya shige dakin sa ya baje saman kafcecen gadonsa yana faman sakin numfashi na farinciki da jindadi har barci barawo yayi awan gaba dashi. ***** sosai take jin gabanta na faduwa tun daga nesa idanuwanta take kara warewa sosai daga cikin motarta har ta iso wajan tayi parking gabanta na tsananta faduwa. 'Innalillahi wa inna ilaihir raji'un'. Ta fadi tana mai daura hannu akai tana mai rushe da wani irin kuka. "Khairiyya". Ta kira sunanta da wata irin muryar mai cike da tashin hankali da tsananin kaɗuwa isa tayi gareta tana janyota daga cikin ciyayin da take rintse idanuwanta tayi lokacin da ta ga mugun halin da take ciki. "Na shiga uku ni Layla wani irin mugun abu nake shirin gani a filin duniyar rayuwa ta ne". A daidai lokacin hannun Khairiyya yayi motsi ganin haka ya sanya ta jijjigata amma ina ba alamun zata iya ko da sake motsi a halin da take sai dai numfashin da ke fita daga hancin ta cikin yanayi na tsananin wahala da yanke rayuwar duniyar nan. Kuka sosai Hajiya Layla ke yi tana faman kiran sunan Khairiyya amma ina ba alamun motsawa da sauri ta sungume tayi motar ta da ita cikin tsananin tashin hankali har zuwa lokacin hawaye ba su daina zuba a idanuwanta ba zuciyarta na faman karyewa da wani irin yanayi mai girma na tashin hankali. "Alhaji Mati-Dr.Erena". Ta fadi cikin yanayi na takaicin zuciya da ruhi sosai ta zauna kan set din motar tana hada kanta da Sitiyari wani numfashi take saki a wahale mai tsananin zafi da ku na. "Ban san rashin imanin naka ya kai haka ba, ban san baka da tausayi har haka ba, ban san abin da yasa na yarda har na san ka a rayuwata ba, ban san mai yasa na anshi bukatarka ba, in da nasan kudirin da ke ranka kenan ba zan taba yarda har hakan ta faru ba". Numfashi taja kafun ta cigaba cikin muryar kuka. "na tsani kaina na tsani rayuwarta da nayi da kai a duniyata Alhaji Mati ban san har lamarin naka ya kai haka ba ban san da wani ido zan kalli yarinyar da na saka hannu wajen KETA HADDI a gareta ba ban san wata irin tsana za tayi mani ba in har tana da sauran rayuwa a duniyar nan kaico na kaicon wannan rayuwa kaicon haduwa da irin ku Alhaji Mati a wannan duniyar na tsane ka na tsane duk mai hali irin naka na tsani sake ko da ganin fuskar ka ce a wannan rayuwa". Hannu ta sa ta dauke zafafan hawayen da take jin su kamar za su dauke mata fatar fuska kafun fuskarta ts kara tamkewa kamar Alhaji Mati na gabanta. "ka tsuwa maye ni Alhaji Mati na rantse maka da Allah sai ka ga ne kurin ka sai na mai da Khairiyya mace sai na mai da ita mai 'yanci sannan kuma da hannunta za ta dauki fansa ka jira lokacin ka Alhaji Mati yana nan tafe". Ta karashe idanuwanta na zubda hawaye kafun ta saki wani murmushi mai ciwo a zuciya da ruhi. Juyawa tayi ta dubi Khairiyya wani kuka ne ya zo mata da sauri ta dake kafun ta fizgi motar ta cilla saman titi gudu take yi kamar zata tashi sama... ******* A hankali ta dago fuskarta tana kallon Get din da zai kaita cikin ABDURRAZAQ FASHION CLUB COMPANY. ba za ta iya shiga ba da yanayin da take ciki a fuskarta ba zata iya zuwa ta kalle shi ba ba ta san mai za tayi masa ba a daidai wannan lokacin in har suka hadu a waje daya. Da sauri tayi wa Motar Key cikin wani irin yanayi na tashin hankali amma fuskarta wani murmushi yake bayyana a kanta juyar da akalar motar tayi ta cilla saman titi kamar zata tashi sama haka take zabga gudu. *KAMALA MINNA*😘😘 [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA ASHIRIN DA HUDU. "Ban san ya zanyi ba Baseera, Ban san mai ke damun zuciyata ba, sosai da sosai nake jin zuciyata wani iri, komai nake ji yana sauya mani a filin duniyata kamar bani ce ba". Ajje numfashi take tana faman tura laɓɓanta duka cikin bakinta tana cizawa fuskarta na kara ya mutsewa kamar mai shirin fashewa da kuka a hankali ta goge gumin da ya taru a goshin ta bayan ta ja gwauron numfashi. "Shekara daya fa...haba mana Baseera ya dace ace ko wani irin laifi akayi wa mutum yayi afuwa". Ta sake fadi tana jin zuciyarta na wani irin duka kadan-kadan. "Ban san laifina har ya kai haka ba...ba ma wannan ba, wallahi ban san mai ma nayi masa ba har ya yi fushi da ni har haka..anya kuwa Baseera Dr.Karami bai manta dani a filin duniyar rayuwarsa ba akan abin da yake ganin babban laifi ne nayi a garesa har ya yanke mani wannan hukuncin wanda yake kokarin tarwatsa komai nawa haba!...". sosai take jin kanta ya shiga sarawa duniyar ta ji tana juya mata komai taji yana kwance mata kamar ba nata ba a hankali ta dago fararen idanuwanta da suka fara kaɗawa zuwa ja laɓɓanta sai faman ƙarkawa suke kadan-kadan yanayin ta ya nuna gaf! take da rushewa da kuka hakan ya sanyata tsagaitawa da maganar da take yi. "Tun tafiyarsa Baseera...tun dan ya bar kasar nan nakasa kwanciyar hankali a filin duniya ta ban son ace ya tafi da bacin rai na a duniyar rayuwarsa ba, ban so ace tun waccan lokacin na fara bata masa rai ba, ban so ace alherin sa garemu na mai da masa da bacin rai ba". Baseera da tun dazu ta zabga tagumi tana duban Mariya da take ta zaro zance cikin rashin hayyaci kallo daya zaka yi mata ka karanci yanayin damuwar da take ciki itama sosai da sosai jikinta da komai nata yayi sanyi. A hankali ta shiga gyara hijabinta cikin yanayi na sanyin jiki kafun ta kau da kanta daga barin kallon Mariya domin ji take kamar ta rushe da kuka ganin yanayin da ƙawar ta ta take ciki ta sani Mariya ta jima cikin yanayin damuwa ta shafe lokaci mai tsayi lamarin na sukar mata zuciya ba tare da ta bayyana hakan ba sai dai in abun ya matsa mata take shiga damuwa sosai har fuskarta ta sauya a nan zaka gane tana cikin wani hali Mariya akwaita da ZURFIN CIKI ba komai nata take fadi ba ba komai dake zuciyarta ake saurin ganowa ba tana da daukon abu a zuciya irin mutanan nan ne masu boye duk yanayin da suke ciki suna da kokarin boye SIRRI komin girmansa. "Na sani Mariya kina cikin yanayi amma hakan bai dace ace kin saka rayuwarki cikin damuwa har haka ba as your age ya kamata ace kin mai da hankali sosai akan wannan karatun da kike yi bai dace ace Tension ya fara samun masauki a filin zuciyarki ba a yarda kike kwakwalwarki ya kamata ace saukaken lamari take dauka ba wanda zai hargitsa komai na ta ba". Nisawa Mariya tayi tana mai sauke wani murmushi mai zafi a zuciya. "duk abin da kika gani a filin duniyar nan tawa na karuwa har izuwa matakin da nake yanzu SHINE SILA Baseera ya kamata ki san da hakan". "Na sani Mariya ba sai kin yi mani tuni ba amma hakan ba wai yana nufin don yana fushi dake ba kuma ki lalata komai abin da baki sani ba shine ya kamata ace kin mai da hankali akan komai musamman karatun nan ina mai tabbatar miki duk ranar da ya sako kafarsa kasar nan to abin da zai bukata shine ya kika kasance bayan tafiyarsa shin kin dauki abubuwan da duk yake miki da muhimmanci ko kuma dama can ba wani martabarsa kike gani ba to hanya daya ce shine ki mai da hankali kan komai da komai da kika san na karuwa ne kuma shine sila kamar yarda kika fadi to ki mai da hankali akan su na tabbata in ya dawo duk wani laifi naki zai kau in har kika cika masa alkawarin da kika daukar masa". Shiru tayi tana dubanta tun da ta fara magana take kallon bakinta ta sani maganar Baseera akan hanya take sai dai kuma bata tunanin maganganun za suyi tasiri azuciyarta domin tashin hankalin da take ciki a filin duniyarta ba ta tunanin zancen wani ba na Dr.Karami ba za su sanya ta cikin natsuwa. Gyaɗa kai ta shiga yi kamar wata ƙadangaruwa sai faman jan numfashi take. "Tashi mu tafi Mariya zaman nan a nan ba zai yi mana ba ki dubi fa kowa ya gama tafiya mu ne kadai mu ka rage". yawatawa da idanuwanta ta cigaba da yi a filin makarantar kafun ta dubi Baseera da ta mike take saɓa jakar ta gami da daukar sauran littatafan ta a hannu ita ma mikewa tayi ta sungumi littatafan ta suka doshi get. "ni ban san ma abin da ya motsa miki tunanin Dr.Karami ba kwana biyu na lura kin rage amma tun da muka fara Exam din nan shikenan komai ya zama sabo fil! kuma hakan ba karamin nakasu zai kawo miki ba ba fata ake ba amma yakamata ace kin mai da hankali wajan Exam din da muke ba wai tunanin wani lamari ba wanda ba ki san ranar karewarsa ba". Gyaɗa kai kawai take yi tana jin zancen Baseera wanda ba ta tunanin zai iya yi mata komai a halin da take ciki. "Shikenan". Ta furta murya can kasar makoshi. ******* Da Sallama a bakin ta ta shiga cikin gidan. Kamar ko yaushe yau ma dai Da'irar aka kafa sai baza idanu ake yi ana kallon mai shigowa da ficewa. Kofar dakin su ta kai wa kallo ganin Umma bata nan zaune hakan ya tabbatar mata tana cikin dakin domin ita dama Al'adar tace haka in dai su Goggo Marka na tsakar gidan nan to bata da filin shan iska a cikin sa in kuwa ta zauna ta san sauran. "nikam cikin kwanakin nan gabadaya Mariya ta canza anya kuwa?". Hafsi ce ta fadi can kasar makoshi tana duban Goggo Marka da ta kafe Mariya da kallo tana binta gaɓa gaɓa kamar wacce take neman wani boyayyan abu. "Allah yasa ba mugun abu ta kunso ba". Hafsi ta sake fadi tana kallon Goggo Marka cikin yanayi na son tace wani abu da zai karawa gulmar ta ta matsayi har ta kara rurata. "Ke nima fa na so ganin haka 'yar Albarka duk naga ta ɗashe tayi fari ga shi ta rage walwala kai jama'a Allah yasa ba mugun abu ta kunso ba mu ga karshen BIRI BOKO da ake yi mana da fankama wai karatu ake yi ita ga mista ƙyanƙyan 'yar gidan mangwafan". Muryar Abulle ne da ta fito daga makewayi ya sanya su yin mukus. Fuskart da fara'a take duban Mariya. "Ahh Yar gidan Umma har an ta so kenan". Mariya da hankalin ta gabadaya bai wajan su jin muryar Abulle ta yi saurin tsayawa tana sakin yaƙe. "Inna ina wuni". Ta fadi tana durkusawa gabanta cikin yanayi na girmama. "Lafiya lau Mariya ya karatun dafatan dai ana mai da hankali?". Gyaɗa kai tayi ba tare da ta ansa ba. "To maza aje a cire kayan a huta Ummanku ta ce mani Jarabawa ku ke ko? to Allah ya taimaka ya ba da sa'a gami da nasara". "Ameen". Mariya ta ansa ta na mikewa ta karasa shiga cikin dakin da Sallama a bakin ta. Abulle dake ta faman sakin murmushi jindadi ganin yarda Mariya take duk sai taji ta burgeta sosai a hankali ta gyaɗa kai tana duban Hafsi wanda suke bin ta da kallo Uku ahu da sauri suka kau da kai. "Ke yanzu ba ki ji kunya ba don Allah ki dubi Mariya ke ba abin kiyi sha'awar ta bane yarda take a natse komai tana yin sa cikin hankali". ta fadi cikin yanayi na bacin rai sosai a fuskarta wani takaicin Hafsi take jin yana tokare mata zuciya ji take yi kamar ta rufe ta da duka. "To sababba nuna min Mariya tafi Hafsi a wajan ki da kike cewa ita abin sha'awa ne da burgewa a hakan ki ka san mugun abin da take aikatawa kawai ta mai dake sauna da sunan tana zuwa makaranta ke kuma ki yarda nan kuwa tsiyarta take kitsawa". Dama ta san za ayi haka shiyasa tun farko bata so cewa komai ba abin ne yake ci mata zuciya amma duk da hakan ba za ta fasa fada masu gaskiya ba don haka ta dubi Goggo Marka murya a tausashe. "Haba Goggo ZATO ZUNUBI fa ko da ya kasance gaskiya ne ke kin san Mariya ba zata yi wannan wautar ba yarinya ce mai hankali ni zan iya shedarta wallahi akan kula da kai". "To naji ita kuma 'yar taki ballagaza ko". Goggo Marka ta tare ta a zafafe har tana kumfar baki. "Nace ita Hafsi ai bata da natsuwa Zainabu ki kiyaye ni bar ganin kin tara su Hafsi hakan ba zai hana ni kwaɗa miki mari ba wallahi don na lura mugun halin naki na nan irin na su baki son laifin su kamar su ne suka sunkuto ki duniyar nan". Sosai Abulle taji zafin maganar don haka ta dubi Hafsi dake ta faman turo baki gama ita ala dole anyi mata ba daidai. "ke dai kin ji kunya wallahi ba fata zan miki ba amma wallahi sai kin yi takaici duk ranar da kika ga Mariya ta zama wani abu a filin duniyar nan da karatun nan nata da kuke ma kallon hadarin kaji...". "Tsine mata nace in baki tsine mata ba ba ki cika ke ce ba yar bakin fata kawai ki san Allah Abulle ki kiyaye ne akan takurawa Hafsi da kikeyi acan gidan naki in taje ba ki kyale ta ba haka in kika zo nan gidan ki sakata gaba da hayyata haba! sai kace ba kya ki ka haife ta ba wannan kiyayyar har ina". "Haba mana Goggo daga fadin gaskiya ni fa tsakani da Allah bana jin dadin yanayin da kike nuna min akan Hafsi ita kenan ba a isa a fada mata gaskiya akan abin da take yi na ba daidai ba kullum ita kenan cikin SANGARTA ni dai ba zan dauki haka ba ya kamata ace ta tsaya ta kula da kanta ita 'ya mace ce...". "Innalillahi wa Inna ilaihir raji'un". Goggo Marka ta fadi kafun ta dora. "Zainabu me kike yi haka ba dai mugun abu kike kokarin daukowa 'yar taki ba nikam Marka ina ganin lalata yau ina ganin mugun abu". Hannu ta daura akai ta rushe da kuka kamar wanda ka zagarwa uwa nan da nan Hankalin Abulle ya tashi takaici da bakin ciki suka turnuke ta shiyasa sam! bata son zuwa gidan nan domin in dai ta zo ba sa rabuwa ta dadi kuma duk akan Hafsi ne. "kiyi hakuri Goggo ni fa ba abin da nake nufi kenan ba ta ya ya zan yi wa 'yar da na haifa mugun fata Allah ya tsareni ya tsari baki na da furta kalmar batacin gareta". "Ke dalla can rufe mani baki ai dama tuntuni na lura kin fi kaunar makiran can akan mu ni da 'yarki ke kenan kullum baki yi mata abun kirki sai dai fada da kushe a haka ki ke so ta dinga zuwa wajan ki a haka kike so ta dinga miki kallon uwarta bayan bakya kaunarta". Sababi na kin kari ta cigaba da yi tun Abulle na danne zuciyarta har idanuwanta suka kawo ruwa da sauri ta zari mahaifinta tana bata hakuri ta bar gidan zuciyarta cike da bakin ciki da takaicin abin da MAHAIFIYARTA take yi mata akan 'yarta. Umma da Mariya da tun da suka ji hayaniyar suka leko ganin abin da ke faruwa ya sanya su tsayawa daga bakin kofa domin sun san in har suka takka kan su komai zai koma a shiga kwashe musu Albarka. Sosai Umma taji rashin jin dadi a zuciyar ta ganin halin da Abulle ta bar gidan da hawaye wanda ta tabbata na bakin ciki ne da takaici ba komai ba. Ba ta san mai yasa Goggo Marka ke haka ba sam haka bai dace ba ya kamata ace tana baiwa Abulle matsayin ta na Uwa ga Hafsi domin nuna mata hanyoyin da suka dace ba wai ita Goggon Marka ta dinga nunawa Abulle bata isa da Hafsi ba hakan ba karamin ganganci ba ne domin ta tabbata Hafsi ba zata taba ganin Mutuncin uwarta ba sai tafi ganin Goggo Marka da mutunci akan uwarta hakan sam bai da ce ba AKWAI ILLA! sosai da sosai a ciki. "Umma mana". Mariya ta fadi da sauti tana mai jinjiga Umma ganin tayi nisa a tunanin. Dubanta tayi tana ajje numfashi mai karfi ta shiga gyaɗa kai kafun ta juya ta koma cikin dakin fuskarta na kara bayyanar da damuwa sosai da sosai. "Ban san wacce irin rayuwa bace wannan ake yi, Ban san mai zan kira wannan rayuwar ba, mai dauke da son zuciya da son kai, sosai ake shiga hakkin zainabu wanda sam hakan bai dace ba ita uwa ce fa ya kamata, ace ana bata hakkinta da damarta akan Hafsi domin 'yarta ce dole ta kula da rayuwarta komai ya same ta ita zata fi kowa kuka akan abin da ya faru da 'yarta haka in abin farinciki ne ya same ta zata fi kowa son haka maganar gaskiya ya kamata Goggo Marka ta daina irin haka SANGARTA da take sanya Hafsi nayi ba zai haifa musu ɗa mai idanu ba". Numfashi Mariya taja tana komawa gefe tana zaunawa hannayenta duk biyu a haɓarta ta zabga tagumi tana duban Umma cikin yanayi na rashin abin cewa ta tabbata da Goggo Marka zata ji wannan maganar kila cewa zatayi Umma ta kafurta ta a filin duniyar rayuwar musulunci gyaɗa kai tayi kafun ta sake duban Umma. "Allah ya kyauta". Da sauri Umma ta dube ta jin abin da ta ce cikin yanayi na son karin bayani. "Umma mu bar maganar nan don Allah a nan in ma son yin ta kike yi gwanda ki je gidan Inna Abulle kuyi domin na tabbata in kika ce wani abu kwaɓarki ce za tayi ruwa wallahi". "Amma Mariya Anya rayuwar zata kasance a haka 'Ya mace ce fa ita Hafsi din nan gaba so take yi a kira ta Uwa anya kuwa hakan za ta kasance haba mana ake duba da idon basira ana daura abin da ya dace a MIZANIN HANKALI...". Cikin yanayi na gundura da batun Mariya ta haɗe hannayenta waje guda alamun roko tana kara marere ce fuska kamar za tayi kuka ba abinda take tsoro illa Goggo Marka ta sani ba za a kwashe ta dadi da ita ba in har ta ji wannan batun... "To Almunafunfun masu lissafa zunubai da ladan bawa tare da yanke masa hukunci shiga aljanna ko wuta ina shiryayyin 'yar taki". Kamar daga sama suka tsunkayo murya Goggo Marka a kofar dakin su tana kokarin shigowa wata irin zabura Mariya tayi tana komawa can gefen katifar daki inda Mu'azzam ke kwance yana barci tana duban Umma da taja wani Numfashi mai girman gaske tana sauke idanuwanta a kofar dakin. A daidai lokacin da Goggo Marka ta bankaɗo labulan kamar zata tsinke ta ajje shi gefe ta karasa shigowa wani kallo ta watsa musu su duka. "Ai duk ɗan da bai san darajar tirelan itace ba to uwarsa bata dumame da wankan jego kuma sanin darajar 'Ya yake sanya iyaye rikon ta ko da ta aikata ba daida ba". 'Yaa hayyu Yaa kayyum'. Umma ta fadi tana mai dafe kanta da take ji yana juya mata yana wata irin sarawa kamar zai rabe gida biyu idanuwanta lokaci guda suka kada sukayi jajir sosai da sosai taji zuciyarta da kasan ruhinta na wani irin tururin zafi kamar an rura wutar makera. A hankali take jan numfashi da take ji kamar zai samu a rauni a tattare da ita sosai take jin wani irin tashin hankali na ziyartata komai na duniyar rayuwarta taji yana canzawa maganganun Goggo Marka ba karamin tayar mata da hankali sukayi ba sosai ta lura shaguɓe da haibaici ta watsa mata wanda hakan ba karamin sanyata cikin ɗacin rai yayi ba gyaɗa kai ta shiga yi cikin rashin abin yi. "wai har mu za nuna wa bariki a filin duniyar nan ni ban san lokacin da dan yawo da shanu jeji jeji ba har ya san bariki...ko da yake ba abin mamaki bane tunda kullum ana zarya da gantali a ko wani titi da layi na cikin gari ana koyon kissa da yarda barbaɗaɗɗun mutane ke yi ba shagon gardawa ba a gidan caca". Hawaye suka zubowa Umma lokaci guda ba tare da ta ba su dama ba, tashin hankalin da take jin kanta aciki a wannan lokacin yafi gaban kwatance sosai take jin wani iri a zuciyarta sosai take jin wani abu mai girma ya tsaya mata a kirji sosai take jin wani irin yanayi mai tattare da kayan takaici da bakin ciki tun daga kasan ruhinta har zuciyarta. Ba za ta iya cigaba da sauraron wadannan bakaƙen kalaman ba. Zuciyarta..Zuciyarta da kwanyarta sosai take ji ba za su iya daukar tashin hankalin dake cikin kalaman Goggo Marka ba ba ta san lamarin tsana da ƙyarar da take yi akanta har ya kai haka ba, ko da yake ba abin mamaki ba ne in dai Goggo Marka ne za ta iya fiye da haka. "Nace wani Kullin ku ka jefi 'yata dashi ta sanyawa 'yarta karan tsana a filin duniyar nan, gabadaya na lura natsuwa da hankalin Zainabu ya na kan ku ko ku ne kuka yi nakudarta sai haka". Ba ta san mai zata ce ma taba a wannan lokacin, ba ta mai ya dace ma tace da ita ba domin komai ya gama kwance mata ta gama tsinkewa da lamarin Goggo Marka. Hawaye ne suka shiga zubo mata ba ƙanƙautawa kanta a kasa lamarin yana kara sanyata tashin hankali dukan ya yi yawa ta lura Goggo Marka so take yi ta kashe ta da ranta ta kunsa mata bakin cikin da zai sanya zuciyarta bugawa. "Da ke fa nake kikayi banza dani Habeeba kisan Allah zan baki mamaki sai na shayar dake ruwan tashin hankali ba dai ki dauki damarar tsayawa a rayuwata ba da ta 'yata mu zuba shege ka fasa a tsakanina dake". Ta na gama fadin haka ta juya tana huci kamar kububuwa ta bar dakin. Mariya da tun dazu jikinta ke ƙarƙarwa hawaye na zuba ganin irin cin mutuncin da ake wa Umma gabadaya ta shiga tashin hankali mai tsananin gaske zuciyarta na faman yi mata zafi da raɗaɗi kamar zata faso kirji ta yo waje. Kuka ta rushe dashi mai tsananin zafi da sanya zuciya tashin hankali , kuka take yi da dukkanin yanayin da ta samu kanta a ciki, kuka take yi da duk wani tashin hankalin da zuciyarta ke dauke dashi. "wannan wani irin BALA'I ne, wannan wani irin tashin hankali ne, Yaa Allah...". Da sauri ta tsaigaita jin wani sabon kuka ya zo mata dunkulewa tayi waje guda tana haɗe jikinta hannunta guda ta tura cikin baki tana cizawa ji take yi komai kamar ba a gaske ba jin komai take yi kamar A MAFARKINTA ba a zahiri ba. "Ya isa haka Mariya". Umma ta fadi da wata irin murya mai dauke da tsananin rauni da damuwa. "Haba mana Umma wai don Girma Allah haka za mu ci gaba da zama ana gaya miki irin wadannan bakaken kalaman ba tare da laifi ba tsakani har ga Allah Goggo Marka ba ta k...". "Nace kiyi shiru ko Mariya". Yanayin zafi mai zurfi da ya fito a muryarta ya sanya Mariya sakin sabon kuka mai cike da haushi. "Ban san mai yasa har yanzu baki san rayuwa ba, Ban san mai yasa har yanzu baki san abin da duniya ta kunsa ba na lura har yanzu baki san kaifaffan ALKALAMIN ƘADDARA ba a duniyar rayuwar dangin rai". numfashi taja tana jin yarda zuciyarta ke kara matsewa waje gudu da tashin hankali mai girma. Sakanni ta kwashe kafun ta sake numfasawa. "ƘADDARARMU CE haka Mariya ya kamata ki san wannan duniya tamkar makaranta take rayuwar da muke yi jarabawa ce mai matukar muhimmanci bai kamata tun yanzu ki karaya da wannan rayuwar ba bai kamata ace tun yanzu ki nuna kosawarki akan ALKALAMIN ƘADDARAnki ba ki sani duk wani rai da yayi saura a filin duniyar nan yana DA SAURAN KALLO ita fa rayuwar nan dama uku ce farko tsakiya karshe misali farko shine haihuwa ki san wannan tsakiya kuma baki san abin da ALKALAMIN ƘADDARA zai dauko miki ba karshe kuma mutuwa ce wanda take tamkar riga a jikin ko wani bawa kullum tana makale dashi har ranar da zata dauke shi". Sosai Mariya kukan ta ya ragu tana duban Umma da jin irin kalamin da take sanar da ita cikin murya mai laushi da kokarin kwantar da hankali gareta sosai take jin zuciyarta na sassautawa komai na raguwa HAWAYEN ZUCIYA da take jin suna kona mata ko ina na kirjin ta suna raguwa. "Mariya ki koyi rayuwar zaman duniya DUNIYA MAKARANTA CE mai girma wacce tafi ko wacce makaranta dake cikinta ba abin da ba a koya a cikinta na dadi da akasinsa sannan a makarantar duniya akwai fannoni masu zafi kuma akwai masu sauki kamar yarda kike ganin salo a makarantun da kike zuwa kamar jarabawa ce in kayi karatu ka jajirce sai ka samu nasara amma in ka saka wasa a lamarin sai ka rasa gane kan komai". Gyara zama tayi sosai tana duban Umma bayan ta tankwashe kafafuwanta kamar mai shirin cin abinci hannayenta a haɓarta ta zuba mata ido. Murmushi Umma tayi kafun ta sake motsa laɓɓanta da salo na rarrashi. "Na shiga cikin yanayi na cuta bayan na warke na rasa miji na kafun nan kuma ga halin da nake ciki tare da Goggo Marka kin ga duk wannan ALKALAMIN ƘADDARA ta tuni ya rubuta su da izinin Rabbil izzati za su faru dani tun kafun na zo duniya". "UKU BALA'I kenan". Mariya ta fadi can kasar zuciyarta da wani irin yanayi mai zafin gaske domin ita dai ba abin da za ta kira wannan lamarin sai haka ba ta hango alheri a cikin su ba sam! balle ta ce musu UKU ALHERI. "Karki dauki wannan a matsayin bala'o'i ki dauke su a matsayin jarabawa da kuma abin da ALKALAMIN ƘADDARA ya rubuta miki TUN FIL'AZAL da sahalewar ubangijin". Da sauri Mariya ta dubi Umma tana ware ido gani take yi kamar ta jiyo abin da ta ke zantawa da zuciyarta. "Sannan ki sani ba ko wacce Ƙaddara ba ce take samun bawa hka kawai sai da sanadi ko sila sannan kuma akwai abubuwa da yawa da suke faruwa a filin DUNIYARMU wanda da yarda mu da sanadinmu komai ke faruwa damu sosai muke daukan wasu abubuwa da suke faru damu mu jinginawa ƙaddara bayan da saka hannunmu komai ke faruwa shiyasa ake so komai DAN'ADAM zai yi a filin rayuwar duniyarsa ya dinga dubawa yana daurawa a MIZANIN HANKALI kafun ya aikata shi, saboda gujewa kuskure domin KUSKURE DAYA TAK! yake saka mutum a da na sani". Sosai jikin Mariya yayi sanyi hawaye kadan-kadan suka shiga zubo mata ji take yi kamar JIRWAYE Umma ke yi mata da zantukanta ba wanda ta tuna a wannan lokacin sai Dr.Karami da fushin da yayi da ita ta tabbata ita ce sila ita ce sanadin faruwar komai amma kuma ai ba ta san sanadi ba ba ta san abin da ya sa yayi fashi da ita ba har haka. "Kan Uban can ke! Habeeba". Kamar daga sama sukaji Goggo Marka ta lailayo ashar ta kudunma ta daura da fadin haka sosai gabansu su duka ya fadi. "Yaa Rabbi?". Umma ta fadi tana mai sakin wani murmushi mai ciwo a zuciya. "Ni za ku mai da 'yar iska ko". Ta sake fadi tana fadowa cikin dakin hannun ta rike da zanin atamfa da ya sha jiki kallo daya zaka yi masa ka gane mugunta da aka yi masa reza ce aka saka aka kekketa shi ketawa wanda baza ta bari a sake morarsa ba. "Uban waye yayi mani wannan mugun abun?". Ta fadi tana mai duban Umma kafun ta sake idanu akan Mariya da tayi mata kuri da idanu tana jiran Sharrin da zai biyo baya don ta lura TUTAR MAKIRCI ce ta motsa. "Da ku fa nake yi ku ka yi mani carko carko da ido kamar kwarto ya fada dakin suruka ya rasa dan kamfansa". Ajiyar zuciya suka saki su duka zuciyarsu da wani irin yanayi mai sanya ɗaci a kasan zuciya da ruhi. "in ban da bakar mugun ta da bakin sharri yanzu Mariya saboda an koya miki bakin hali irin na dangin uwarki shine zanin nawo kika kama ki ka kekketa sabo mugun abu". 'Yaa Salam!'. Umma da Mariya suka fadi a zuciyoyin su Ba su an karaba sai kawai saukan mari Mariya taji a kuncin ta ji kake kau!. "Dan uban uwarki Lamiɗo ne ya saka ki yi mani mugun halin nan ko billahillazi sai kin biyani in ba haka ba na dake ki dukan shan gishiri". Tana gama fadin haka ta jefa mata zanin a fuska ta juya tana watsa wa Umma wani makirin kallo da tukuicin tsaki sannan ta fice daga dakin. Hawaye suka ciccko a idanun Mariya ta shiga gyaɗa kai ganin irin kallon da Umma take yi mata mai kama da TUHUMA. "BA NI BA CE". "Na sani". Umma ta fadi tana mai sakar mata murmushi kafun ta kau da kai tana dauke Kwallar da suka kawo idanunta farmaki... *KAMALA MINNA*😘😘😘 [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA ASHIRIN DA BIYAR. 💕 *_Ki Karba. ki Koya, Idan Kalma So Ta Amsu Yarda Ke Tabbatar Da Kauna._* 💕 -Usaini Danko. A hankali take sauke jakar dake rataye a kafaɗarta cikin yanayi na sanyi jiki idanuwanta na kan kayan da ta gani zube tsakar dakin tana yawatawa idanuwanta akan su cikin yanayi na son sanin daga in da suka fito domin wani irin bugu taji gabanta yayi lokacin da idanuwanta suka sauka kan kayan. Motsa laɓɓanta tayi da take jin suna cijewa kamar ba sa son ta motsa su. "Umma wadannan kayan daga ina kuma?". Ta fadi har zuwa lokacin idanuwanta na kan kayan ta dubi Mu'azzam da ya koma gefe ya tasa choculat gaba yana faman gabza. "Uhmm!". Ta sake fadi tana mai duban Umma da tayi tagumi fuskarta da yanayin damuwa dago idanu tayi ta dubi Mariya da gabanta ke ci gaba da bugawa kamar zuciyarta zata faso kirji ta fito. "Uhmm baki hadu da Yayan naki bane?". Cikin yanayi na rashin fahimta take duban Umma da son nuna bata sani ba gyaɗa kai tayi a hankali tana mai samun waje tana zama don ji take yi kamar kafafuwanta ba za su iya daukarta ba sosai yanayin ta ya canza lokaci guda ta shiga tura laɓɓanta cikin baki tana cizawa gabanta take ji yana kara tsinkewa gaɓadaya tun da ta tashi yau take jin wani iri a jikinta kasala da rashin son magana duk su ne suka zama abokan hirarta ko da taje makaranta yau haka ta wuni sukuku Baseera ba yarda ba tayi ba akan ta fadi mata abin da ke damunta amma fir! ta nuna ita ba abin da ke damun ta kawai ba ta jindadin garin ne yau. Lamarin yayi tsamari yanzu don sosai da sosai take jin faduwar gabanta na daɗuwa. Wani numfashi Umma ta ja tana fesarwa kafun ta dubi Mariya da tayi sakato da baki tana dubanta alamun son karin bayani. "Ban san mai kike nufi ba Umma. Wani Yayan nawa ne ya zo?". Murmushi Umma ta saki mai dan zurfi don ta lura Mariya a dan ruɗe take kamar wani abu na damunta. "Hashim mana". 'Yaa Allah'. Mariya ta fadi tana mai kai hannayenta duk biyu tana dafe kanta idanuwanta lokaci guda suka dan kaɗa domin yanayin da take ciki ta kosa ta ji inda Umma ta dosa da zancen domin har yanzu a duhu kanta yake ta rasa gane in da lamarin ya dosa. Duban kayan ta sake yi tana mai yarfe hannunta da ta cire daga baki kamar wacce ta taɓa wuta. "Ban gane ba Umma waye haka?". Wani irin kallon Mamaki Umma take bin ta dashi cikin yanayi na rashin zaton maganar Mariya din sosai take dubanta da yanayi na bata so abin da Mariyar tace ba numfashi ta ja kafun ta motsa laɓɓanta a raunane. "Yaa Allah mai kike nufi Mariya ba dai har kin manta alheri ba ba dai zaki ce dani kin manta dashi a filin duniyar rayuwarki ba haba! mana yaushe har yaushe hakan zai faru ina! fada min shekaru nawa kuka dauka da rabuwarku dama akwai wannan rana Yaa Salma Haba mana Mariya karki saka zuciyata ta buga mana karki canza mana daga yarda na sanki". Sosai rauni ya bayyana a muryar Umma bakin ta na rawa har ta dire furucin ta tana duban Mariya da wani irin yanayi mai dauke da daci sosai a zuciya fuskarta lokaci guda ta shiga sauyawa tana rinewa da wani irin abu mai girman gaske. Tsoro ne sosai ya bayyana a idanun Mariya lokaci guda idanuwanta su kayo waje sosai tana duban Umma da su yanayin da ta ganta a ciki da bacin rai yayi matukar daga mata hankali ba kadan ba da sauri ta mike kanta na wani irin dokawa kamar zai rabe biyu gaban Umma ta karasa ta durkusa kwalla suka cika mata idanu lokaci guda laɓɓanta suka shiga ƙarƙarwa kamar wacce ruwan sama yayi wa dan banzan duka. "Don Allah Umma...". "Ya isa haka mana Mariya". Umma ta tare ta a zafafe tana mai daga mata hannu da wan irin yanayi mai bayyanar da bacin rai kafun ta ja numfashi mai zafi ta dubi Mariya wacce a lokacin hawayen su fara digo mata. "Ban san haka ki ka koma ba, Ban san yaushe ki ka fara canza halayenki ba, Ban san mai yasa kike kokarin daukar hali na manta Alheri ba, sosai nayi mamaki sosai naji wani iri a raina ban yi tsammanin hakan ba ko A MAFARKINA". Shiru tayi tana maida numfashi kafun ta dora da cewa, "Nayi tunanin dama akwai abin da kikayi masa a lokacin baya kafun ya tafi na daɗe ina zargi haka banyi zaton samun haka ba a gareki Mariya Yaa Allah". Rikicewa Mariya tayi lokaci guda kamar wata zautacciya tana duban Umma cikin yanayi na bayyanuwar tsoro a idanuwanta. "Wallahi ban san wanene ba, ban san akan wa ki ke magana ba don Allah Umma kiyi hakuri ina nan a yarda kika san ni ban sauya halayena ba komai na nan a yarda kika sani na daga halayena na san ALHERI ban mantawa da wanda yayi mani shi". "Bana tunanin haka, ba yarda za ayi ki ce mani baki manta da shi ba na yarda domin ga shi nan kin nuna na gani don haka...". "Umma Please mana". "Kin manta Dr.Karami ko Mariya kin manta mutumin da ya yi...". "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un Astagfurullah wa'atubu'ilai". Abin da tayi saurin ambata kenan tana mikewa tsaye hannunta a goshin ta wani irin hajijiya take ji anayi da ita komai taji yana kwance mata a lokacin runtse idanu tayi komai taji ya na dawo mata a shekara daya da rabi da suka gaba komai take ji kamar yanzu yake wakana fatanta Allah yasa ba fushin nasa bane har yanzu ba ta san ya za tayi ba in bai yafe mata ba bata san wani hali zata shiga ba in bai yi mata afuwa ba. 'Yah Dr.Karami ya zo'. Ta ambata da wani irin yanayi a zuciyarta wani irin bugu taji zuciyarta tayi a hankali ta sauke hannayenta tana dafe kirjinta da su Umma take duba kafun ta dubi kayan da suke jibge tsakar dakin Mu'azzam da ya gama shan sharafin sa da chocolut duk ya bata jikin sa ya tashi yana takawa a hankali kamar mai tsoron ya fadi saboda rashin kwarin tafiyar tasa. "Da gaske Umma? Yaa Allah! Yana ina Umma don Allah yana ina fada min". Yanayin da take magana da rawar jiki wani murmushi mai kauri yana samun mazauni a fuskarta zai tabbatar maka kamar ba a hayyacin ta take ba jin komai tayi a hargitse a daidai wannan lokacin. Sosai Umma ta dube ta tana shirin gasgata yanayin da Mariya take nunawa na rashin sanin Dr.Karami ya zo da farko ta dauka rashin hankali zata nuna mata kamar ta mance dashi shiyasa gabadaya taji wani iri a ranta matuƙa domin kuwa a duniyar nan bai kamata ace Mariya ta mance Dr.Karami ba ko da kuwa shekara nawa zai yi ya dawo. "Ya koma". Ware ido tayi tana duban Umma. "Yaa Hayyu Yaa Kayyum! me yasa yayi mani haka Umma mai yasa ya tafi ba tare da ya tsaya mun ga juna ba shin ya mace shekara da muka dauka har da rabi ba tare da mun sanya juna a idanu ba bai kamata yayi min haka ba haba! Umma mai yasa ba ki ce yaje makaranta ba ko kuma ya jirani na dawo". Muryarta tayi rauni kamar mai son fashewa da kuka a hankali ta fara kokarin zubewa kasa domin jin komai take yi yana sauyawa komai take jin ya narkewa na jikin ta kafafuwanta take jin su kamar ba za su iya daukar gangar jikinta ba. 'Ban san laifi na ya kai har haka ba, ban san abin da na aikata yayi tsamari haka ba, ya kamata ace ka tausaya min kayi mani uzuri akan abin da ban san na aikata ba haba mana! haba mana!'. Zuciyarta ta shiga fadin kalamai kamar mai shirin zaucewa sosai take jin wani irin zafi na tururi suna wanzuwa a zuciyarta da kasan ruhinta. Ba ta san ya zata fassara yarda take jin wannan lamarin ba bata san ya zata fassara yarda take jin akan yanayin da Dr.karami ke nuna mata ba sosai zuciyarta da dukkan jikinta ke shiga tashin hankali mara yankewa. Cikin yanayi na rashin fahimta Umma ke dubanta fuska na bayyanar da tausayin da take ji akan 'yarta ta ta sani dole ta ji ba dadi ta jima da lura da yanayin Mariya akan Dr.Karami shakuwa ce mai girman gaske Allah ya halitta a tsakaninsu wacce rabuwarta take da matuƙar hatsari a junansu musamman Mariya da ta zurfafa lamarin ta bashi matsayi mai girman gaske a filin zuciyarta. "Assalamu alaikum! Wai ana sallama da Mariya". Kamar daga sama suka jiyo amon muryar yaro daga tsakar gida. Umma ta dubi Mariya ita ma ita take kallo. "Waye?". Umma ta fadi da sanyin murya har lokacin idanuwanta na kan Mariya da tayi fakare tana zazzare ido fata take yi Allah yasa Dr.Karami ne. "Wani ne a cikin mota". Zabura Mariya tayi ba tare da wani jinkiri ba ta sa kai za tayi waje. "Mariya!". Umma ta fadi da sauti tana mai tsayar da ita Cak! ta tsaya jikin ta sai faman rawa yake yi kamar wacce aka kaɗawa gangi. "Ban so abin da kikeyi haba mana Mariya sai kace wata karamar yarinya ko wacce bata da kamun kai meye haka yanzu ke da wannnan yanayin zaki fita shin kin san ko waye yake kiran ki kin san yarda zaki taddashi ba kya tsoron kallon da zai miki na rashin kamun kai ban yarda ba don haka dawo". Ji tayi kamar ta daura hannu aka ta rusa ihu don takaici da haushi hana ta fita da akayi domin zuciyarta sai tsalle take yi tana sanar da ita ta fita shine ya zo nemanta. Jiki a sanyaye hawaye na kokarin zuba mata ta samu gefe ta zauna tana wasa da hannayenta. "Ke haka zaki girma ko da rawar kai ana yabon ki sallah alwala zata gagari ki wannan wacce irin wauta ce sai kace ba 'ya mace ba ki ke irin wannan haukar to ba zan lamunta ba kin ji ko tun wuri ki daina hakan tun kafun ya zame miki jiki ai kewar mutum ba hauka bane...ba ma wannan ba yanzu dake ki barin jiki zuwa ganinsa ki na da tabbacin shine". Kasa takara yi da kai tana girgizawa zuciyarta na kara matsewa a filin kirjinta so take yi kawai ta ganta a wajan nan. "Maza tashi ki wanke wannan fuskar taki". Ba musu ta mike tayi waje ji take yi kamar ta zura da gudu amma tana tsoron bacin ran Ummanta don haka tana wanke fuskar ta dawo ta zauna tana ajje numfashi kadan-kadan. "ki goge fuskarki ki tashi ki tafi". Umma ta fadi da Umarni a zuciyarta cikin yanayi na daure fuska sosai. Ba musu mafiya tasa ta goge fuskarta har tana muttsuƙa ɗan basilin kafun ta mike bayan ta zare kayan makarantar dake jikinta ta saka doguwar jallabiya da hijab sannan ta sa kai ta fice. A hankali take taku tana jin gabanta na dokawa duk takun daya sai taji ya karu sosai a haka har ta isa soro nan ta ja burki ta tsaya tana mai da numfashi a hankali ta shiga kokarin daidaita kanta. Motarsa dake girke gefe guda take sauke idanuwanta akanta sabuwa ce fil! sai daukar idanu take yi kamar yanzu aka gama ƙerata bakin glass din ta mai duhu wanda ya boye sirrin komai na cikin motar sosai taji gaban ya doka lokacin da ta fara takawa cikin sanyi jiki zuwa wajan motar ba abin da take ambata a zuciyar sai sunayen Allah. "Yaa Rabb!". Ta furta lokacin da wani kamshi mai karfi ya daki hancinta har sai da ta kusan dauke numfashi gabanta yayi wani irin bugu ta shiga ware idanu cikin yanayi na tsoro a fuskarta hannayenta biyu ta saka ta dafe goshinta da take ji kamar zai fice gefe daya wani irin abu ne taji zuciyarta ta buge ta dashi da bata yi tsammani ba dago idanunta tayi ta na saukewa akan motar a daidai lokacin shi kuma ya buɗe murfin yana zuru kafafuwansa masu dauke da wani haɗaɗɗen takalmi sau ciki mai kalar baki sai daukar idanu yake yi. Gabanta ya cigaba da dokawa tana kara ware idanu so take yi ta karyata zuciyar da idanuwanta da suke kokarin wanzar mata da abin da ba tayi zato ba ko kadan a daidai wannan lokacin ba ta fada abin dake shirin faruwa a yanzu ya faru ba haka take so ba bashi tayi KUDIRI ta gani ba a daidai wannan lokacin. "Dr.Aqeel". Ta fadi da wani irin yanayi mai zurfi a zuciyarta da gangar jikinta numfashi take kokawa dashi da yake kokarin yanke mata tashin hankalin ta take jin ya karu ba kadan ba ba ta shirya ba bata shirya karbar wani tashin hankalin ba bayan wanda take ciki mai yasa zai mata haka mai yasa zai katse mata hanzarin ta mai yasa ya zo a daidai irin wannan lokacin da bai dace sam dashi ba mai yasa?. A hankali ya gama fitowa yana mikewa kan kafafuwansa idanuwansa na kan Mariya dake tsaye kamar wacce aka dasa kwankwarar motsi ba tayi illa numfashinta da yake fita da sauri-sauri fuskarta a haɗe kamar hadarin dake shirin zubda ruwa a hakan kuma take yaƙe wanda yafi kuka ciwo. Murmushi a fuskarsa mai girma duk da glass din da ya mannawa idanuwansa hakan bai hana ta hango tsakar idanun nasa ba kau da kai tayi da sauri tana jin yarda zuciyarta ke bugawa cikin wani irin yanayi mai girma in ba ta manta ba rabon ta dashi yau kusan wata shidda kenan tun wani zuwa da yayi da wani lamari mai girma da ta kasa fahimtarsa tun daga lokacin ya dauke kafarsa da zuwa gidan su da sunan ya bata lokaci tayi tunani akan lamarin da ya zo mata dashi Alal-hakika ta mance da wanzuwansa duk da dai tana jin sa a ranta amma abin da ya zo mata dashi tuni ta ajje shi gefe domin ita a tunanin haukar ta ba zai dawo ba tsokanar ta yake yi a sigar wasa amma ganinsa a yanzu ya dawo mata da komai tsoronta daya ya tuhumeta bata san mai zata ce dashi ba bata san ma ya za tayi da maganar ba domin ko a MIZANIN HANKALIn ta da ta daura bata ga komai ba. "Mariya". Ya fadi yana kara ƙawata fuskarsa da murmushi sanye yake da Suit light Blue wanda tayi matukar amsar jikinsa sosai hannu rike da hula mai kama da malfa baka haka takalmin kafarsa baki ne sai kyallin sabuntaka yake yi. Tun daga kafafuwansa ta fara kallonsa har izuwa kirjinsa sosai shigar tasa ta burgeta ba kadan ba sai dai turaren da ya fesa ne yake hawa mata kai sosai ji takeyi kamar zata yi amai. "Dama kai ne?". Ta fadi tana mai tura laɓɓanta gabadaya cikin bakinta cikin wani irin yanayi na karfin hali. Dubanta yayi cikin mamaki da kuma tuhuma yana sauke glass din idonsa sosai yake kallonta yana karantar yanayin da yake ganin ta a ciki sosai ya fuskanta kamar da matsala a tattare da ita lakari da yanayin da yarda ta nuna na rashin hayyaci a tattare da ita kuma ga idanunta da fuskarta a haɗe kamar hadari. "Ba kiyi tsammani ba ko?". Ya fadi yana daga mata gira da murmushi a fuskarsa kafun ya sake cewa, "Akwai wanda kikayi tsammanin gani kenan ba ni ba?". Ya sake jeho mata tambayar da ta sanya cikinta kaɗawa domin gabadaya a tsora ce take. "Uhmm!?". Ya sake fadi yana mai jingina da jikin motarsa bayan ya rufe. Shiru ya gifta a tsakaninsu ba wanda ya sake cewa komai Dr.Aqeel dubanta yake yana jiran cewarta yana harɗe hannayensa a kirjinsa Ita kuwa gabadaya ba ma ta san ya take ba komai nata a kwance yake laɓɓanta sai motsawa suke yi alamun ta na son cewa wani abu amma ta gagara idanunwanta har zuwa lokacin a kasa suke. "Dr.Karami ya zo ko?". Da sauri ta dago kai tana dubansa jin abin da yace idanunwanta take yawatawa a nasa wani abubuwa ne masu matukar girma take gani suna fitowa suna doso ta daga idanuwansa da sauri ta janye idanunta tana faman kokawa da numfashin ta da ke kokarin kufce mata. "Uhmm nima yanzu na dawo makaranta Umma ke fada min amma ba mu hadu dashi ba". Ta karashe tana yarfe hannaye kamar wacce ta taba wuta. Sosai ya fuskanci ruɗanin da take ciki sosai ya gane in da yanayin da tashi ya dosa wato Dr.Karami tayi tunanin ya kira ta shi yasa ta fito cikin yanayi na hanzari amma ganin sa da tayi ya sanya komai nata kwancewa. "Shi kika son gani ko Mariya, Dr.Karami kika so ki gani bani ba, na sani domin na gane hakan a tattare dake". Sosai yaji wani irin abu mai girma ya tokare masa zuciya. Ya fuskanci Mariya hankalinta da natsuwarta suna tare da Dr.Karami tun da yake zuwa bai ta ganin rawar jiki ko wani ɗoki ba a game da ita amma yanzu ya gane in da tafi wayo sai dai kuma ba zai yarda da hakan ba. "Mariya!". Ya fadi da wata irin murya mai girma da zurfi da abubuwa masu yawa a ciki. Ita kanta wani yanayi taji da salon da ya kira sunan nata komai taji ya zama kamar ruwa na jikinta yana narkewa zuciyarta ta yi wani irin zillo da wani abu mai girman gaske wanda ta jima tana a jiyarsa a zuciyarta a tsakaninta da Dr.Aqeel wanda har izuwa wannan lokaci bata san menene ba. Sosai ya gyara tsayuwarsa don ji yake yi kamar zai tiku da kasa kansa yake ji yana sara masa da wani irin yanayi mai zafi bai san haka zata faru ba da bai bata lokacin sa ba da ya san haka zata kasance da ya mika bukatarsa tun wuri sosai da sosai zuciyarsa ta jima tana gargaɗin sa akan yayi abin da ya dace amma yayi ragwanci shi a tunanin sa ya raina yanayin Mariya bai san ba a nan lamarin yake ba yana cikin filin zuciya domin ita zuciya ba ruwanta da kankanta ko girma in ta nuna so da kulawa a abu to tabbas hakan ne. Nisawa ya yi kafun ya furzar da wani huci mai zafi. "Mariya wai shin mai ke damun ki ne ko dai ni din ne ba kya bukatar gani a filin rayuwarki?". Ya fadi da wani irin yanayi mai zafi da nuna bacin rai hakan ya sanya Mariya saurin dagowa tana dubansa lokaci guda wani haske mai kama da kibiya ya fito daga idanuwansa ya sauka a nata. 'Yaa Rabb!'. Ta furta jin yarda zuciyarta ke amsawa da wani irin yanayi mai girman gaske. Girgiza kai ta shiga yi alamun ba haka bane. "haka ne ma na gashi nan kin nuna min tun da na zo gabadaya na ga sauyawarki komai naki ya canza kamar bakya maraba dani ko na lura bani kika yi tsammanin gani ba nayi miki shigar sauri ". "Kayi Hakuri Dr.Aqeel". Ta fadi da rauni a muryarta kamar zata saki kuka laɓɓanta take motsawa alamun ta na so ta sake cewa wani abu amma zuciyarta taki bata dama. "Ba maganar bada hakuri bane Mariya so nake yi ki buɗe baki sannan ki dube ni muyi magana so nake yi komai ya kasance a wannan lokaci so nake yi duk wani SIRRIN DAKE RAINA ki ji shi a yau so nake yi komai da yake cikin zuciya ki ji shi da kunnuwanki so nake yi ki bani dama na shigo rayuwarki mu kasance a INUWA DAYA". A razane ta dago kai tana dubansa gabanta na daɗa faduwa ji take yi komai na duniyarta a lokacin yana wurgi da ita ta ko wani fanni ba ta san mai Dr.Aqeel yake kokarin dauko mata ya jeho mata a filin duniyar rayuwarta ba bata san wani irin tashin hankali bane yake kokarin jeho mata. Tsoron ta ya karu sosai ta shiga gyaɗa kai wasu kwalla ne taji su na taruwa a idanuwanta wanda bata san dalilin su ba sosai zuciyarta take matsewa da zancen Dr.Aqeel wanda ba ta san yarda zata fassara yarda suke kasancewa a zuciyarta ba. "Mai zai hana ki karba Mariya sannan ki koya kuma tun da nasan baki iya ba baki taba yi ba wannan shi First time dinki a cikin wannan lamarin ya kamata ki bani dama da yarda na tabbatar miki na san zaki karba kuma ki koya a lokacin da kika bani hadin kan ki na bayyana miki SIRRIN DAKE RAINA". Zuciyarta taji ta yi wani irin harbawa gabadaya ta dago mata kirji sama hannu tasa ta dafe kirjin nata ji take yi kamar ta kurma ihu ko ta samu sa'ida amma ina ba za ta iya yin haka ba bata san mai ALKALAMIN ƘADDARARTA ke kokarin dauko mata ba da ya jona ta da Dr.Aqeel da wannan lamarin mai girman gaske. "Ban san me kake nufi ba, ban san ina zancen ka ya saka gaba ba don Allah Dr.Aqeel...". "Haba mana Mariya me yasa zaki fadi haka mai yasa kike kokarin dauko abin da kika san ba zan taba yarda dashi ba na sani kin ji ni sa rai kuma kin fahimta kawai karba ne ba zaki yi ba saboda baki yarda dani ba". "Yaa Allah! haba mana Dr.Aqeel mai yasa kake fadin haka mai yasa kake kokarin kasa fahimta ta da ganga bayan kuma kasan ba haka lamarin yake ba". Sosai yaji jikinsa yayi sanyi da maganganun Mariya dubanta yake yi da wani irin yanayi mai girma a zuciyarsa kafun ya nisa. "Mariya mai zai hana mu fahimci junamu mu bai wa zuciyoyinmu damar fahimtar tsakanin su hakan ne kadai zai sanya lamarin da muke fuskanta ya zo mana da sauki a filin duniyar nan ta mu". "Ta ya ya kake zaton haka zai kasance bayan kasan ni ba kowan kowa bace a duniyar nan". "Ba abin da nake so naji daga gareki ba kenan Mariya ki daina kauce hanya yakamata ki tsaya a mataki daya wanda zai kawo mana mafita a tsakaninmu". Shiru tayi tana tunanin abin da za ta ce dashi zuciyarta ta rabu gida biyu hankalinta ya karkata izuwa wajan Dr.Karami shi take bukatar gani shi take bukatar sanyawa a idanunta a wannan lokaci tafi bukatar dashi da kowa so take yi su gamu da juna ba ta san wani matsayi ya ajje ta ba bata san ko har yanzu ya na fushi da ita ba zuciyarta ta na sanar da ita har yanzu yana nan kan bakarsa tun da har ya iya zuwa bai neme ta ba kuma ya san inda zai same ta amma yayi birisda ita dan hakan tana cikin TSAKA MAI WUYA domin ta lura da Umma ita kanta ta nuna bacin ranta nunawa da tayi bata gane Dr.Karami ba to ina ga kuma ta san halin da suke ciki a tsakaninsu na bacin rai da ta sanya shi. So take yi ta gujewa tashin hankalin da Dr.Aqeel ke kokarin turata a ciki domin kuwa zuciyarta gabadaya ta hargitse kwanyarta sai tururi take yi. "Ki bani lokaci mana a lokacin da ke cikin rayuwarki na sani zaki fahimce ni nan gaba kadan". Gƴaɗa kai take yi cikin rashin abin cewa bata san abin da zata ce dashi ba ta sani Dr.Aqeel yayi mata HALACCI bai kamata ta watsa masa kasa a ido ba bai kamata ta mance ALHERI da yayi mata ba a filin duniyar rayuwarta ba ma ita kadai ba har da iyayenta sai dai zuciyarta ba ta san matsayar da zata ajje shi ba bata san a wani matsayi yake ba a cikinta. "Shikenan". Ta fadi da wani irin nauyi mai girma a zuciyarta domin ita dai ba ta san mai zata ce dashi ba bata so ta fadi abin da zai sanya shi bacin rai ko ya tafi da fushin ta a zuciyarsa bata so ayi na biyu kamar Dr.Karami. Gyaɗa kai kawai yayi yana mai sakin yaƙe sosai ya fuskanta Mariya na bukatar lokaci sosai take matakin koyon komai da yake nuna mata zai yi kokarin don ganar da ita komai yarda ya kamata ba ya so yayi sake a cikin wannan lamarin. "Sai anjima ki gaida su Umma". Ya fadi da murya mai sauti wanda tayi matukar tasiri a zuciyar Mariya ta saukar mata da kasala. Tana kallon shi ya shiga motarsa ya bar layin tana bin sa da kallo har ya bacewa ganin ta kafun ta ja raunannan jikin ta ta koma cikin gida zuciya cike da rikici mai yawan gaske... *_KAMALA MINNA_*😘😘😘 [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA ASHIRIN DA SHIDA. Ta jima sosai cikin soron gidan nasu tana jan numfashi, yanayin da take jin kanta a ciki a wannan lokacin ba zata iya cewa ga yarda yake ba ta san dai tana cikin wani irin yanayi na rashin natsuwa gami da ciwon rai. Bata san ya zata yi da Dr.Aqeel ba bata san mai ya kamata tayi masa ba zuciyarta take jin tana shiga wani irin mataki mai raunin gaske yana haifar mata da yanayi na shiga ruɗani sosai take jin wani fili a zuciyarta ya na baiwa Dr.Aqeel matsayi da kalamansa wanda take jin su sun fi komai daga mata hankalin a wannan rana. Hannunta daya ta saka cikin baki tana cizawa kafun ta fiddo shi tana yarfewa fuskarta na ya mutsewa da wani irin yanayi mai girman gaske a gareta. Ta jima kafun ta fara jan kafafuwanta da take jin su kamar ba nata ba kamar ba jikinta suke ba sosai take jin gajiya a cikin su ji take yi kamar za su watsar da ita kasa a hankali ta kai hannunta ta dafa bango tana tafiya a hankali har ta karasa shigewa cikin gidan. "Na ce karuwanci kike koyawa 'yarki tana bin gardawa kamar wata karya kin ce ba haka ba yanzu me ne ne wannan Iyee nace yanzu menene wannan ai duk wanda ya ga wadannan kayan ya san da walakin goro a miya ba yarda za ayi a dauki wannan uba uban kayan a baku su haka zikau ba tare da kuma an ci ribar ku ba". Maganganun da suka shiga dukan kunnuwan Mariya kenan a daidai lokacin da ta iso tsakar gidan ta tsinkayo muryar Goggo Marka cikin dakin su wani tashin hankali ne taji zuciyarta da kwanyarta sun dauka lokaci guda sun tsaya cak! da aikin da sukeyi lokaci guda duk wani magudanan jinin ta suka tsaya komai nata take jin sa ya sauya ji take yi kamar ba a duniyar nan take ba ji take yi kamar ba RAI DA RUHI a gangar jikinta juwa taji ta fara daukarta lokaci guda ta durkushe a wajan cikin wani yanayi tana mai jan numfashi da k'yar yana fizgar kansa shi kuka take so tayi amma zuciyarta da idanuwanta sun ki bata damar haka sai zafi da raɗaɗi da take jin sunayi kamar zasu tayar da kan su daga gareta. Hannayenta ta saka a saman kirjinta tana shafawa domin ji take kamar ya tarwatse gabadaya idanuwanta a runtse a hankali ta fara kokarin tashi tana jin yarda kirjin nata yayi mata wani irin nauyi da abu mai girman gaske wanda take jin yana rinjayarta. "Kin ce 'yar ki makaranta take yi ita ga wacce ta fi kowa son ilmi ko yanzu tsakanin ki da Allah Habeeba wannan shine makarantar da take zuwa don na tabbata a hanyar fitar da take yi ne ta hadu da wanda yayi mata wannan hidimar kuma na tabbata ba haka kawai bane sai da ta biyasa kafun ya bayar". 'Yaa zuljalalu wal'Ikram Ya Hayyu Yaa Kayyum'. Abin da take jin wani sashi na zuciyarta na fadi kenan har ta iso bakin kofar ta tokare hannayenta a saman goshinta ji take yi kanta kamar zai tarwatse idanuwanta a runtse ta shiga ajje numfashi mai girma gaske wani abu taji ya zo mata makoshi ya tsaya tana jin yarda yake kartar mata ko ina na kirjinta har zuwa makoshi. "Haba mana Goggo Marka ta ya kike tunanin zan jefa 'yar da na haifa a cikina cikin wannan mugun yanayi ribar mai zan samu a ciki". Muryar Umma ta tsinkayo ta fadin haka muryarta cikin yanayi mai kama da kuka da sauri ta dago kanta ta ware idanunta kafun ta dage labulan dakin tsaye ta hango Goggo Marka sai faman tsaki take ja tana jifan Umma da mugun kallo jin motsi ne ya sanyata juyowa ganin Mariya ya sanya ta sakin wani murmushi na mugun kafun ta shiga tafa hannayenta. "Uhmm a hakan kamar gaske musa a baki fir'auna a zuci". Ta fadi tana yatsine fuska kafun ta dan rangwafa inda kayan suke tana bincike kafun ta shiga ware wasu a gefe guda sai da ta ware masu isarta sannan ta sunguma tana duban su Umma. "To mu ma dai bari mu ci albarkar kacin bariki ko kin san ko ina kayan alheri suke dadi gare su Allah ya karo mana irin su masu kyautatawa". Ta na gama fadin haka tayi hanyar yo wa waje Mariya da tayi sumar tsaye bangazar da taji anyi mata ya dawo da ita hayyacinta a rikice ta dubi Goggo Marka sannan ta dubi Umma wacce ta zabga tagumi hawaye sai shatata suke yi a fuskarta bakin ciki da takaicin duniya duk sun cike mata zuciya gabadaya ta hargitse sosai fuskarta ta ke nuni da tsananin tashin hankalin da take ciki ganin Mariya na dubanta ya sanyata saurin dauke hawayen da suke zubo mata tana sakin wani yake wanda yafi kuka ciwo. Wani irin kuka ne Mariya taji yana zo mata a daidai wannan lokacin hannu ta saka ta toshe bakinta tana karasawa cikin dakin durkushewa tayi gaban Umma da wani irin yanayi na tashin hankali mai girman gaske laɓɓanta na rawa ta shiga motsa su. "Na Shiga Uku wanna wacce irin rayuwa ce take kokarin tunkaromu a daidai wannan lokacin wannan wani irin yanayi ne mai sanya ciwon rai ya sanyo mu gaba". Hannu Umma ta daga mata alamun tayi shiru kafun ta fara magana cikin yanayi na rauni. "Ni ban ga abin shiga uku ba don haka ki daina ambatar mana Uku a nan kin ji ko kina dai bata hawayenki ki share su domin in har kika ce zaki cigaba da zubda su to na tabbata zaki shekara dubu a haka in dai kina cikin wannan rayuwar duniyar nan". Fakare tayi da kunnuwa ta zubawa Umma idanu kamar wacce taga bakuwar fuska kafun ta shiga jan hanci kamar zata fizgeshi daga fuskanta. "Haka nake nufi domin kuwa in har kace ba zaka dauki abin da ALKALAMIN ƘADDARA ya kawo maka rayuwa ba to kana tare da tashin hankali mai girman gaske". Hawaye suka sake balle mata domin ji tayi komai ya kwance mata zuciyarta na wani irin zugi da raɗaɗi. "Amma Umma..". "Haba mana Mariya". Tayi sauri katseta kafun ta ja numfashi da take jin sa da wani irin yanayi mai zafi gaske. "Ina kika baro shi". Runtse idanu tayi jin zuciya ta bugu kafun ta ciza laɓɓanta tana jin wani abu mai nauyin gaske na danne mata kirji da zuciya. "Ba shi bane". Ta fadi a raunane kamar zata fashe da wani sabon kukan wanda ya fi wanda ta gama ciwo. Ware idanu Umma tayi cike da mamaki jin abin da Mariya tace. "Kamar ya bashi bane to waye?". Kamar ba zata ansa ta ba sai kuma tana ja numfashi ta fesar. "Dr.Aqeel ne". Duban sosai Umma ta shiga yi mata kamar mai son karin bayani akan abin da ta fadi yanayin da ta nuna ya tabbatar mata akwai abin da yake faruwa ganin sai yatsi ne fuska take yi tana cizon laɓɓa. "Me ke faruwa na ga sai dakune fuska ki ke yi?". "Bakomai yace yana gaishe ki". "Mariya!". Umma tafadi cikin wata irin murya mai zurfi har sai da gaban Mariya ya yanke ya fadi dago idanuwanta tayi da suke kasa ta dubi Umma da tayi mata kuri da Idanu da tuhuma cikinsu. "Akwai abinda ke damun ki bayan Dr.Karami ki fada min ina bukatar sanin ko mene ne na gaji da wannan halin da kika aro ki ka saka a filin rayuwarki wanda sam! ban ga amfaninsa ba". Gyaɗa kai ta shiga yi kamar zata rushe da kuka zuciyarta da kwakwalwarta take jin su kamar za su kama da wuta saboda wani irin tashin hankali mai dauke da turiri take ji yana wanzuwa acikinsu. "da ke nake magana Mariya na gaji fa". "Umma!". Ta fadi cikin wani irin yanayi da rauri a muryarta kafun ta nisa ta na cizon laɓɓanta. "ba abin da yake damu na...". "ban yarda ba...shikenan ma komai ya shige ki bar komai a zuciyar ki hakan daidai ne". Umma ta fadi tana mai kokarin mikewa kayan dake tsakar dakin ta shiga janyewa tana ajewa gefe guda ganin haka da Mariya tayi ta san Umma haushin taji shiyasa ta rabu da ita da sauri ta mike tana kokarin taya Umma kwashe kayan hannu ta daga mata ba tare da ta kalle ta ba. "Bar shi kawai ki zauna ki yi tunanin abin da ya dace ki fidda kan ki daga damuwar da kike ciki tun da bakya bukatar abokin shawara a filin a rayuwarki". Jikin ta lokaci guda yayi sanyi jin abin da Umma tace hannu ta sa tana goge kwallar da taji sun kawo mata ziyara idanuwa. "Kiyi hakuri Umma..". "ni ba kiyi mani komai ba Mariya ki je ki zauna ki huta ni na bukaci haka". Ba yarda ta iya domin yarda ta ga Umma na maganar ta san har kasar zuciyarta don haka a hankali ta ja jiki ta zauna in da Mu'azzam ke kwance yana faman barci abun sa. Bata san mai ya dace tayi ba, ba ta san mai ya kamata ace tayi a filin duniyar rayuwarta a yanzu ba komai take ji yana sauya wa komai take ji yana canzawa a filin rayuwarta ji take yi kamar ba ita ba jikinta take ji yana yi mata wani iri kamar wacce bata da lafiya zuciyarta take ji tana yi mata nauyi kamar wacce aka daura dutsen dala. Ta jima cikin wannan yanayin kafun ta lura da har Umma ta gama kwashe kayan ta bar mata daki hannu bibbiyu ta daura a fuskarta ta zabga tagumi domin kuwa gabadaya take jin tunanin ta ya tsaya komai na ta ya tsaya cak! ba abin da take hangowa sai tashin hankalin dake gabanta yanzu bata san ina Dr.Karami yake ba a yanzu tsoron ta daya kar ya sake komawa ba tare da sun hadu da juna ba. ******* "Umma Zan je gidan su Baseera". Mariya ta fadi cikin yanayi na fargaban abin da Umma zata ce domin tun jiya da ta shareta har yau bata sake tsayawa sun yi wata magana mai tsayi ba bayan gaisuwa da tayi mata da safe. "Allah ya kiyaye hanya ki gaida Hajiyar ta Baseera". Abin da ta fadi kenan ba tare da ta dube ta ba hakan ya sanyayata jikin Mariya ta shiga gyaɗa kai da susar gefen fuskarta kafun ta shiga motsa baki. "Umma don Allah kiyi hakuri...". "Mariya haba mana nace miki bakomai ki tafi kawai". Jin abin da tace ya sanya ta duban Mu'azzam dake hannun Umma hannunta kai ta shafi fuskarsa tana sakar masa murmushi kafun taja jiki ta fice daga cikin dakin. A tsakar gida ta tsaya tana gyara hijabin dake jikinta domin ji take yi kamar bai zauna daidai ba a hankalinta juya ta dubi bangaren su Goggo Marka Hafsi ta hango tsaye daga ita sai daurin kirji kamar wata uwar mata ta kafe ta da idanu tana faman yatsine fuska kau da kai tayi kamar bata ganta ba da sauri ta zira takalmanta ta fice daga cikin gidan domin a yarda take jin kanta ba ta bukatar wata magana ta sake shiga tsakanin ta da wani har ta isa gidan su Baseera. Tafiya take yi a hankali domin isa bakin layi ko za ta samu napep din da zai kai ta Unguwarsu Baseera taji take yi zuciyarta da kwanyarta sai faman dauko mata tunani suke yi wanda sam bata so ace sune a kanta ba yanzu. Kamar daga sama taji ana yi mata Horn bata yi tunanin da ita ake ba hakan ya sanyata kara sauri tana komawa gefe duk a tunanin ta wani ne a bayan ta yake mata horn domin ta bashi hanya amma ina ta ji an ci gaba da yi ba kankautawa hakan ya sanyata tsaya wa cak! waje daya tana daga kanta don dubin ganin abin da ke faruwa motar Huzaif ta hango yayi parking yana kokarin fitowa wata irin faduwar gaba taji tana zo mata lokaci guda wanda ita a karan kanta ba zata ce ga dalili. Dubansa ta shiga yi cikin wani irin yanayi wanda ba za ta ce gashi ba amma dai tana jin yarda zuciyarta ke bugawa a dukkanin sakan idanuwanta take yawatawa a kasa tana tunano yaushe rabon ta dashi sun kwana biyu ba su hadu ba sosai ta lura da yanayinsa kamar mara lafiya domin tafiyar ma kamar mai koyanta haka yake yin ta har ya iso in da take tsaye tana faman jan numfashi. Lokaci guda idanuwansu suka sarƙe da juna aka rasa mai dauke nasa tsayin lokaci suna a haka kafun Mariya ta ja dogon numfashi ta fesar fuskar ta cikin yanayi na karan kadahan. "Uhmm Huzaif dama kana duniyar nan". Hakan da ta fadi da yanayin da tayi maganar ba karamin sanya Huzaif cikin wani irin yanayi mai armashi a hankali ya shiga motsa laɓɓansa fuskarsa na wanzar da wani farinciki mai dauke da fara'a jan numfashi yake yi yana fesar wa idanunsa akan Mariya zuciyarsa yake ji tana daukar kanta tana kaiwa wani mataki mai girman gaske yanayin da yake kallon Mariya wani farin ciki da muradan jindadi yake jin sa a ciki. Ya sani yayi kewar Mariya ba kadan ba zuciyarsa tayi jinyar rashin ta sosai ya shiga cikin wani hali na rashin jindadi sosai duniyar yake jin ta wani mataki a kwanakin baya da yake zaune yana jinyar kan sa dalilin rashin lafiyar da ta same shi. " Baki damu dani ba Mariya shiyasa sam rashi na bai d'ad'a ki da kasa ba". Ya fadi yana mai dan haɗe rai kanta ta dago ta dube shi tana mai yatsine fuska kafun ta ja numfashi. "akan mi zaka ce haka wa na sani na ka da zan tambaya ina kake so naje ko so kake yi na bi layi ina cigiyar ka Huzaif bai dace ka yi mani wannan maganar ba sam". Kuri yayi mata da idanu yana kallon yarda take motsa laɓɓanta kalamai na fitowa wani irin farin ciki yake ji yana sake zundumawa a ciki. "Allah ya baki hakuri amma dai zaman tare ai bai ce haka ba ko?". Ya fadi yana murmushi kau da kai tayi tana mai yatsine fuska sam bata bukatar magana ba ta so ace ta sake gamuwa da wani a daidai wannan lokacin ba tafi bukatar su hadu da Baseera domin ita kadai ne take so su zauna domin sanin abin da ya dace ita kadai take tunanin zata fada wa abin da yake kokarin faruwa da ita ko ma tace ya faru da ita... "Ina su Umma da Mu'azzam?". Maganar Huzaif ta katse mata tunanin da ta jefa kanta a ciki. "Uhmm suna gida suna lafiya". Ta fadi tana kokarin raɓashi ta wuce ganin haka ya sanya shi saurin dubanta. "Meye haka kuma Mariya yake kike kokarin tafiya...wai ma ina zaki kike wannan saurin". Yanayin da yayi maganar kamar da bacin rai a ciki ita hakan ita ma ya so bata mata rai jin irin tambayar da yake yi mata kamar shi ne ya ajje ta ba ta ansa shi ba illa duban sa da tayi ta kau da kanta. "Ina Zaki je ne?". Ya fadi ganin kamar ranta ya so baci yayi kasa da muryar. "Unguwa zani shiyasa nake sauri bana so na bata lokaci a bakin titi". Gyaɗa kai yayi yana dubanta kafun ya numfasa cikin d'ard'dar. "muje mana in kai ki ko". Wani duba tayi masa wanda sai da yaji yan cikin sa sun motsa dama ya san za ayi haka da sauri ya kau da kai don ba zai iya jure irin kallon da take masa ba zuciyarsa wani irin yanayi take fadawa mai girman gaske. "Don Allah mana". Ya sake fadi yana mai hada hannayensa waje daya alamun roko. Girgiza kai tashiga yi tana mai taku a hankali za ta bar wajan gabanta yasha yana mai harɗe hannayensa a kirjinsa idanuwansa ana ta tana watsa masa kallon ban son haka. "Mariya wai shin ko laifi na sake yi ne ake kokarin hukunta ni ta wannan hanyar?". "ko daya kawai dai bana ra'ayin abin da ka zo mani dashi ne nagode kawai kayi tafiyarka". Ware idanu yayi jin abin da tace sosai yake dubanta yana kallon yadda ta kara haɗe fuska kamar hadari amma hakan bai hana kyanta ƙara bayyana ba wani irin kwarjini yake ganin tana yi masa wanda ya shagalar dashi ga kallon ta har bai san lokacin da ta raɓashi ta wuce ba. Firgigin yayi ya dawo hayyacin sa ganin bata wajan ya yi saurin juyawa can ya hange ta tayi nisa dashi kadan.'Yaa Rabbi'. Ya ambata yana takunsa cikin hanzari ya isa in da motasa take ya shige tare da yi mata key bayan yayi ribas ya bi bayan ta da gudu cikin yan sakanni ya isa in da take tsaye tana kokarin tsaida wani mai Napep parking yayi ya fito ya iso in da take tsaye suna magana da mai Napep din ba tare da yace mata komai ba yace dubi mai Napep din. "Yi hakuri don Allah yi tafiyarka". Ya fadi yana mai hade fuska da sauri Mariya ta juyo ta dubeshi da wani irin kallo ganin yarda ya hade fuska ita ma sai ta hade. "Ya haka ya za ayi in tsaida abun hawa ka ce ya tafi ina ruwan ka dashi?". Bai tanka mata ba illa nuni da yayi mata da motarsa alamun ta je ta shiga. "Ba zan shiga ba kaji ko Allah ba in da zani Huzaif bana bukatar takurawa bana son abin da zai bata mutuncin junanmu". "kawai Malama ki je ki shiga mu tafi ya za ayi ace ina waje kuma ga abin hawa a tare dani amma ki tare wani mai Napep wannan ai ba mutuncin ki bake". 'Ikon Allah'. Ta fadi a ranta ta na sakin guntun murmushi kafun ta dubi Huzaif da ya haɗe rai kamar wani hadarin dake shirin zubda ruwa. "wai don Allah Huzaif me yasa kake son takura mani ne na ce maka nagode ba zan shiga motarka ba to ka hakura mana". "Ban san wannan zancen ba kisan Allah in har baki shiga mun je ba sai dai mu kwana a nan in zaki tsaida Napep dari sai na kore su". Ware idanu tayi cikin yanayi na mamaki na karfi halin Huzaif ita abin ma dariya ya so ya bata. Bata ga dalilin da zai sanya shi takura mata ba akan sai tayi abin da yake so shi ba mijinta ba shi ba ubanta ba amma ya kafe da bata Umarni. Duban sa tayi ganin ya harɗe hannayenda ya jingina da gaban motarsa sai faman kaɗa kafa yake yi fuska a tamke ba alamun wasa kuma ta lura da gaske yake yi din sai dai su kwana a nan. Wani tunani ne ya fado mata da sauri ta dube shi cikin mika wuya domin ta tabbata maganarsa da ya fadi tsaf zai aikata ita kuwa ta tsani tsayawa bakin titi ba ma wannan ba lokaci tafiya yake yi kuma in har ta jima bata koma gida ba dole ta fuskanci fushi a wajan Umma da ma ya ya ta barota balle kuma yanzu ta kara wani laifin ai sai abin yayi yawa shege da hauka. Tsuke fuska tayi kamar hadari ita ma sannan ta isa wajansa tana mai kau da kai tana turo baki gaba hakan ba karamar dariya ya baiwa Huzaif ba amma sai ya kanne domin ya san in har yayi dariya zainl iya bata shirin nasa a hankali ya dube ta cikin danne dariyar da take kawo masa hari. "To ya yan mata muje ne ko kuma mu cigaba da zama a nan har mahadi ya bayyana?". wata harara ta watsa masa bai san lokacin da ya saki dariya ba har da buga kafa ya isa ya bude mata gidan gama yayi mata alamun ta zo ta shiga. Ware idanu tayi kafun ta kau da kai. "nikam ba zan shiga gaba ba baya zan shiga". Dubanta yayi ganin da gaske take ba za tashiga ba cikin yanayi na zolaya ya dube ta. "Kuturu mana..." "A'uzubillahi minal shaidanir rajim zagi Huzaif". Ta fadi tana ware idanunwanta akansa shima zaro idanu yayi yana faman gyada kai. "Uhm Uhm fa kar ki fassara ni Malama ni ba zagi zan yi ba". Harara ta wurga masa kafun ta isa wajan motar ta buɗe gidan baya ta shige. Dariya yake yi mata ganin yanayin da ta nuna kamar zai hana ta shiga. Shiga yayi shima ya na fadin. "wato kin mai dani direban ki ko?". Ko kallon sa ba tayi ba kanta na bakin kofar tana kallon waje har yayi wa motar key kafun ya tambaya ne ta in da sukayi "Pabeyi". Yanayin da ta fadi sunan Unguwar tana turo baki gaba sai ya bashi dariya ita ala dole fushi take yi dashi da gasken gaske. Tafiya sukayi ta tsayin mintuna biyu ba wanda ya yi magana a tsakanin su ba abin da ke tashi cikin motar sai wakar 'Because of You' ta Amanda Mena sosai wakar ta tafi da hankalin Mariya don sosai taji muryar mawakiyar da yarda take sarrafa kalaman ta sun burgeta lokaci guda taji kaunar mawakiyar ya dalsu a zuciyarta ji take yi kamar ta tambayi Huzaif wace ce ita amma ba za ta iya wannan ganganci ba yanzu ji take yi kamar tana zaune akan k'aya. "Mariya" Kamar daga sama taji muryar Huzaif ya furta hakan gabanta taji ya yanke ya fadi ta madubin gaban motar ta hango irin kallon da yake yi mata ba tare da sani ba ba ta ansa shi ba illa idanu da suka hada da sauri ta dauke kanta tana jin gabanta na cigaba da bugawa. "me yasa wai har yanzu baki yarda dani bane na lura mafi akasari in muna tare bakya sakin jikin dani kamar zan cutar dake". Gyada kai tayi ba tare da tayi masa magana ba lokaci guda ta shashantar da maganar ma ta na nuna masa hanyar da za ta kai su layin su Baseera. "Ya kamata ki bani hankalin ki nan magana nake so muyi ta fahimtar juna a tsakanina da ke". Da sauri ta dubeshi jin abin da yace gabanta lokaci guda ya yanke ya fadi ba wanda ta tuna a wannan lokacin sai Dr.Aqeel da yanayin da suka kasance a tsakanin ta dashi a jiya maganganun sa ne suka shiga dawo mata kamar yanzu suka yi su gabanta ya cigaba da tsanar ta faduwa zuciyarta na dauko mata wani lamari mai girman gaske wanda yake kara sanyaya mata jiki numfashi ta shiga ja a hankali kafun ta sake daga kai ta dubeshi har zuwa lokacin idanuwansa na kanta wani abu mai girman gaske take hangowa a idanuwansa wanda suke ruɗa mata nata idanun da sauri ta dauke kai jin da tayi numfashin ta na fizga kamar zai fice daga gangar jikin ta lokaci guda ta ji nadama ta saukar mata ba ta san abin da yasa ta tsaya da Huzaif ba ta san abin da ya kai ta shiga motarsa ba har yake kokarin firgita ta. "ba zan boye miki ba Mariya ina cikin wani irin hali mai wuyar fassaruwa ban san ta ya ya zan fada miki halin da nake ciki ba zuciyata tana cikin wani hali mai girman gaske Mariya komai na faruwa ne a dalilinki". "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un". Abin da taji bakin ta na fadi kenan daga nan bata san wata duniyar kuma ta fada ba sai da ta shafe sakanni kafun ta dawo hayyacin ta dauke da tashin hankali sosai taji ana hajijiya da ita ji take yi kamar tana saman gajimare ana yawo da ita kwanyarta taji ta tsaya cak! da aiki zuciyarta na wani irin bugu kamar zata faso kirji ta fito a hankali ta dago kanta tana duban kofar motar Huzaif ganin sun shiga layin su Baseera ta fara kokarin tsaida shi domin ya sauke ta a yanayin da take jin kanta ko sakan bata fata ta sake yi a cikin wannan motar domin kuwa ji take yi kamar an daura ta a kan KASKON WUTA. Idanuwanta ne sauka sauka kan wata dalleliyar mota sabuwa fil sai kyalli take yi haska rana na kara haskata hannu ta sa ta rufe idanuwanta domin sosai motar ta haske mata fuska da kyallin haka kawai taji gabanta ya fadi sannan kuma tana son kallon motar ware idanu tayi har motar ta karasa fitowa daga get din gidan su Baseera tana kokarin barin layin sosai take kallon motar har ta iso daidai in da suke shi kansa Huzaif hankalinsa ya tafi wajan motar sosai. "Yaa Allah". Mariya ta furta da wani irin yanayi domin bugun da taji gabanta yayi sosai glass din motar a dage yake kuma gashi mai duhu ba ka gano wanda yake cikin motar hakan ya dan bata ran Mariya duk da tashin hankalin da take ciki ta so ace ta ga waye a cikin motar domin zuciyarta sosai ta kwadaitu da son ganin ko waye. "ajje ni a nan". Mariya ta fadi tana mai dafe kanta da sauri ya dawo da hankalinsa gareta ya dubanta ganin hankalinta bai gareshi hakan ya bashi damar sake kare mata kallo kafun yace. "Ina son magana dake Mariya ki bani lokaci ko ya ya ne". "Please don Allah Huzaif ka barni da naji da abin da yake damu na bani da lokacin da zan iya zama naji abin da zaka fadi don Allah ka kyale ni". Ta karashe tana kokarin buɗe motar ta fice. "Mariya!". Cak! ta tsaya ba tare da ta karasa ficewa ba a hankali ta juya ta dubeshi ganin yanayin da yake ba karamin faduwa gaba taji ba da sauri ta fice daga cikin motar har tana kokarin faduwa ko tsayawa dubansa bata yi ba ta doshi gidan su Baseera cikin yanayi na rashin hayyaci sai faman hada hanya take yi kamar wacce ta sha kaya maye... *_KAMALA MINNA_*😍😍😍 [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA ASHIRIN DA BAKWAI. Mariya ta jima tsaye bakin get domin daidai kanta, sosai ta shiga tashin hankali komai taji yana kwance mata. tsayuwar ta a nan shine kawai take ganin mafita domin in har ta cigaba da tafiya zubewa zatayi warwas a kasa, domin kuwa kafafuwanta take ji suna harɗewa kamar an narka roba. Numfashi take ja ta na saukewa kafun ta sanya hannu tana kwankwasa Get din a yan sakanni mai gadi ya iso sai da ya leko ta 'yar karamar kofar dake jiki ya ga wacece sannan ya zo ya buɗe karamar kofar yana bin Mariya da kallo fuskarsa da fara'a da alamun ya santa dama. Gaidashi tayi kafun ta juyo ta dubi in da Huzaif yake abin mamaki tsaye ta hango shi ya harɗe hannayensa idanuwansa na in da take tsaye saurin dauke kai tayi tana mai cusa kanta cikin gidan bayan ta gaida baba maigadi. Huzaif ganin ta shige cikin gidan hakan ya sanya shi dukan jikin motarsa da wani irin yanayi na tashin hankali mai girman gaske. Zuciyarsa yake ji tana wani karta masa kamar an saka kaifaffiyar wuka ana yayyagawa idanuwansa sun kad'a sun yi jajir kamar wanda akayi wa surace da barkono hannayensa ya daura saman kansa yana dafewa ji yake yi kamar zai tarwatse komai yaji yana kwance masa duniyar yake ji ta ishe shi ba san mai ya dace yayi ba bai san abin da ya kamata ace yayi a daidai wannan lokacin ba akan Mariya. Ya sani zuciyarsa ba karamar wauta da ganganci tayi masa ba wanda bai san ya zai yi ba in har Mariya ba ta dubeshi ta anshi abin da ya zo mata dashi ba dole filin duniyar rayuwarsa ya kasance cikin tashin hankali mai girma. A hankali ya fara taka kafafuwansa kamar wanda kwai ya fashewa a ciki yana jan numfashi da yake jinsa kamar zai gushe masa isa yayi ya bude motar ya shiga sai da ya shafe mintina kansa haɗe da sitiyari domin ji yake yi kamar ba zai iya tukin ba gabadaya a haka ya ja motar yana mai ficewa daga cikin unguwar domin dai ba zai iya tsayawa ba don ya tabbata Mariya ko ta fito ba hawa motar tashi za tayi ba a yanayin da ya ga ta nuna akwai alamun tashin hankali da bacin rai mai girma tare da ita yana zaton laifin sa ne kuma ba na kowa ba da wannan tunanin zucin ya bar unguwar gabadaya. Da Sallama ta shiga cikin babban falon yanayin ta kawai zaka kalla kasan akwai abin da ke damun ta a zuciyarta. Sakanni ta shafe kafun a ansata a bata izinin shiga Tunda ta saka kafarta cikin falon ta lura akwai mutane da yawa a ciki ba kamar daba da take zuwa ta samu Mami kawai ko Baseera amma yau abun ya sauya da alamun anyi bak'i. Ba ta san ta karasa cikin falon ba sai da taji muryar Mami nayi mata sannu da zuwa da sauri ta gayyato natsuwa ta azawa kanta sosai ta shiga cikin wani yanayi ganin duk mutanan dakin ita suke kallo a hankali ta fara takawa ta isa cikin falon sosai tana mai zubewa ta gaishe da Mami sanna ta gaida mace da namijin da taka gani wanda kallo daya tayi musu ta gane suna da alak'a da Mami domin ga kama nan da suke yi da Baseera musamman ma namijin. "Mariya ke ce a gidan namu yau?". Gyada kai tayi tana faman yake don ta san da biyu Mami tayi mata magana na kin son zuwan ta gidan nasu sai dai Baseera taje nasu Mami ta sha turawa Mariya ta zo amma sai taki zuwa amma kuma ba laifin ta bane Umma ce ta nuna rashin yardarta don bata son shige-shigen nan musamman gida irin na su Mami masu farcen susa sai ayi wani tunanin daban ko wani abu ke kawo ta. "Uhmm Mami dafatan na same ku lafiya?". "Lafiya lau Mariya ya su Umman da Mu'azzam". "Duk suna lafiya Umma tace na gaishe ki sosai da sosai". "Madalla ina ansawa". Daga nan ba wanda ya sake yin magana Mariya na son tambayar Baseera don bata ganta a falon ba amma duk sai taji ta kasa nauyin mutanan dake zaune take ji. "Yusra yau dai Allah ya hadaku da 'yar gidan mutuniyar taki ga Mariya nan da ake tayi miki kwakwazo akanta". Wacce aka kira da Yusra din da sauri ta dago kanta daga kan waya fuskar da fara'a kallo daya za kayi mata ka gane JINI DAYA suke da Baseera matashiya ce wacce ba zata haura shekaru talatin a duniya ba da alamun ma tana da aure akan ta domin akwai jariri wanda bai haura wata shidda ba a gefenta yana barci. "Masha Allah ashe dai Aku mai magana ba tayi karya ba Mariya Sannu ko ya su Umma?". Mariya dake sunkuye da kai ta dago tana duban Yusra sosai tana mamakin yarda take yi mata magana cikin sakin jiki da fara'a da alamun dai wannan a jini su yake dukkan su ita ma Mami haka take haka ma Dady da wuya ka ga fushin sa gyada kai Mariya tayi tana ansa ta kafun ta sake gaishe ta fuska ita ma a sake. "Mutuniyar taki tana sama dakinta tun dazu ta shiga ban san abin da take kintsawa ba". Murmushi Mariya tayi kafun ta mike ta bi hanyar da za ta sada ta da dakin Baseera. "Ba ki ji ba Mariya". Mami ta fadi hakan ya sanya Mariya saurin tsayawa ta juyo ta na duban Mami. "wadannan duk yayin Baseera ne wannan shine Babban su Babban d'ana kenan su nan sa Tareeq ita kuma wannan Yusra tana aure a Abuja shi kuma Tareeq yana karatu ne a kasar waje". Gyada kai take yi tana faman sakin murmushi tunda Umma ta fara yi mata bayani mai da kanta tayi kan su tana kara dubansu. Da sauri ta isa wajan Yusra kamar wacce aka tura ta isa wajan jaririyar dake kwance ta shafa mata kai kafun su hada ido da Yusra ta sakar mata murmushi. "Dauke ta mana". Kamar abin da take jira kenan ta sanya hannu ta dauka tana faman sakin yake ita ana ta ganin murnushi take yi kamar wanda aka matsawar baki. "Yah Yusra yariyarki mai kyau kamar Mu'azzam din mu ya sunanta?". Dariya Mami tayi kafun ta dubi Yusra da ta kafe Mariya da ido ganin yarda take barin jiki akan 'yar ta duk sai taji Mariya ta kwanta mata a zuciya sosai da sosai. "Mariya wai dama kina magana haka". Mami ta fadi cikin mamaki. Da sauri tayi kasa da kai alamun jin kunya tana kokarin juyawa ta haye sama. "Sunanta Nawwara". Yusra ta fadi da tausassan murmushi a fuskarta. A hankali Mariya ta juyo ta dube su kafun ta sauke ganin ta kan Tareeq wanda ko kallon ta bai yi ba tun da tashigo har ga Allah taji zafin yanayin da ya nuna mata bata son mutum irin haka mai shariya duk hakan ta dauke shi a matsayin wulakanci ne a filin rayuwarta. Dago kai tayi da zumar barin wajan caraf! suka hada ido da Mami rausayar da kai tayi da alamun ita ma Mami ta lura da halin-ko-in-kula da Tareeq ya nuna don haka tayi mata alamu da ido tayi hakuri kar ta damu. A hankali taja jiki ta bar falon tana jin Yusra na yabata a kan yanayin da ta nuna mata akan Nawwara da ita kanta. A baje ta same ta tsakar gadonta duk ta warwatsa littattafai kamar wacce aka yi wa dole sai ta karance su a lokacin. Mariya bata san lokacin da ta saki dariya ba tana isa cikin dakin sosai. Dariyar ce ta fargar da Baseera da sauri ta daga kai ganin Mariya ya sanya ta sakin wata kara tana dirow daga kan gadon gabadaya tayo kanta ganin haka ya sanya Mariya matsawa gefe don ta san karamin aikin ta ne tace zata rungume ta kuma ga jaririya a hannunta. "Uhm Uhm yau anyi kyan kai kenan, Mariya yau kece a gidanmu?". Ta fadi tana galla mata harara kamar idanunta za su fado kasa. "Uhmm ni fa matsala ta dake wani lokacin hankali yawa yake yi miki yasin baki ganni da Yarinya bane zaki fado kai na". Yatsine fuska tayi kafun ta dubi Nawwara. "Hala Adda Yusra ce ta hadaki da wannan 'yar ta ta mai shegen kuka kamar gyare?". Ware ido Mariya tayi. "Nawwara din ce mai kuka". "Yo eh mana ba ta gajiya da kuka yanzu ma don tana barci ne amma yasin ta tashi ko Hmm sai kin mai da ita wajan uwarta nima abin da ya koro ni daga falon kenan kukanta tun dazu take abu guda kamar cin kwan makauniya". "ikon Allah gani da gajiyawa yo ke duk abin da kike yi ba a gaji dake ba sai kece zaki ce kin gaji irin wannan son kai haka har ina". Dariya Baseera tayi tana mai jawo ta ta zaunar da ita bakin gadon kafun ta juya ta isa wajan da dan madaidaicin firij dake can gefe lemo ta dauko mata da gorar ruwa gami da Cake ta kawo mata da kanta tayi saving din ta amma sai bari Mariya tace ta bari zata dauko ta gode a hakan ma. Sun jima cikin wannan yanayin Baseera sai fama ratata zance take yi kamar wata rediyo cikin maganganun nata ne wata magana ta so narkar da Mariya daga in da take zaune. "wai shin da zaki shigo baki ga wata hadaddiyar mota ta fice daga layin nan ba?". Baseera ta fadi tana mai daukar Nawwara daga jikin Mariya, kaɗa idanu tayi kamar mai tunani kafun ta gyada kai alamun eh ta gani domin ta lura da mota da Baseera ke magana akanta. "Dr.Karami ne ya zo muka gaisa...". Daga wannan batun Mariya ba ta sake sanin in da kanta yake ba gabadaya taji ana juyata kamar waina a tadda tashin hankalin da take ciki taji ya karu sosai sai yanzu ta gane faduwar gaban da tayi dazu da taga motar ashe Dr.Karami ne. Sosai kan ta ya kulle komai taji na tunanin ta ya tsaya cak! Ba abin da ke dawainiya da ita sai mamaki da al'ajabi ta yarda Dr.Karami gabadaya ya sauya yake gujewa haduwarsu ba ta san ya ya za tayi ba ita kam! Ba ta san mai yake nufi da ita ba. "Yace ma jiya a gidanku ya wuni tun muna makaranta yaje ashe". Gyaɗa kai kawai Mariya take yi tana faman jan numfashi kirjinta take ji yayi mata wani irin nauyi mai girman gaske numfashin ma da k'yar take iya jan sa. Jin shirun yayi yawa ya sanya Baseera dubanta sosai da sauri ta ware ido ganin yanayin Mariya dafa ta tayi cikin yanayi na sanyin jiki. "Me ke faruwa ne wai lafiya kike kuwa Mariya naga gabadaya lokaci guda kin sauya ne me ke damun ki". Wani numfashi mai zafi ta ja ta fesar kafun ta dubi Baseera da idanunta masu kwalla cikin rauni ta fara magana tana cizon laɓɓanta. "Kin san kuwa har yau ba mu hadu dashi ba". Ta karashe kamar zata rushe da kuka jin zuciyar ta take tana zafi da raɗaɗi kanta na wani irin sarawa kamar zai rabe gida biyu. Ware idanu Baseera tayi gami da dafe kirji. "Na Shiga Aljanna". Wani murmushi Mariya ta saki wanda ya fi kuka ciwo kafun ta ja numfashi wanda ya haifar mata da wani irin ciwo a zuciya dama duk gangar jikinta. "Ni kuma na shiga Uku Bala'i Baseera". Zabura Baseera tayi ta mike gabadaya kan kafafuwan ta jikinta lokaci guda ya shiga rawa kamar wacce aka jonawa wayar wuta Nawwar dake hannunta har kokarin faduwa take yi duban Mariya take yi cikin wani irin yanayi na ban san in da kika dosa ba dubanta take yi da wani irin yanayi mai dauke da rauni da tausayi dubanta da take yi da wani irin tashin hankali mai girma da ya ziyarci zuciyarta dama dukkannin jikinta. A hankali ta shiga jan numfashi tana mai kokarin kwantar da Nawwara don ta tabbata in ta cigaba da riketa zata iya watsar da ita ba tare da ta sani ba ba abin da ya kara daga mata hankali sai hawayen da ta gani a idanun Mariya suna zuba. "Yaa Rabbi!". Ta fadi tana zubewa bakin gado kamar wata kayan wanki tagumi ta zabga tana ganin ikon Allah wai uwar miji da cin kazar amarci. "Mariya wai shin me ke damun ki ne haka wallahi kin ta yar min da hankali ba kadan ba". Nisawa tayi zuciyarta na wani irin harbawa kafun ta ciji laɓɓanta. "Ban san mai Alkalamin ƙaddarata yake kokarin rubuta mani ba, ban san wani irin tashin hankali ne yake kokarin shigowa rayuwata ba a daidai wannan lokaci Baseera ina cikin matsala, matsala babban wacce ban san maganin taba zuciyata zafi take yi ruhina raɗaɗi yake yi kwanyata ta cushe da tashin hankali mai girma ji nake yi kamar bani ba a filin duniyar nan ji nake yi kamar komai ya sauya a jikina...". "Ya isa haka". Baseera ta fadi jin muryar Mariya ta fara rawa tana kokarin sakin kuka. Ruwa ta tsiyaya cikin glass cup din dake ajje kan farantin da ta kawo mata lemo akai a hankali ta dauka ta mika mata ba musu ta ansa ta kwankwade kamar dama can kishin ruwan take ji wani numfashi taja wanda ya sanya Baseera dubanta da sauri tana mai ware idanunwanta akanta domin gabadaya ta tsorata da yanayin da ta ga Mariyar a ciki. Sun shafe mintina a haka ba wanda ya sake magana a tsakaninsu sai ajiyar zuciyar Mariya kawai sautin ki tashi ita kuwa Baseera kafeta tayi da ido gami da zabga tagumi domin ta rasa ma mai ya dace domin sosai da sosai kanta ya dau caji ba kadan ba. "wai shin har yanzu fushin da Dr.Karami yake yi dake ne duk ya sanya ki cikin wannan halin ko me ne ne?". Baseera ta fadi da wani irin yanayi mai girman gaske a zuciyarta muryarta tayi laushi sosai. Girgiza kai Mariya ta shiga yi cikin rashin fahimta Baseera tace. "To me ke damun ki wai shin?". Sai da taja numfashi mai ciwo kafun ta dubi Baseera. "Sun sako ni gaba Baseera ban san ya zan yi ba ina cikin tashin hankali". "Yaa Allah! sun sako ki a gaba fa kika ce su waye haka me kuma suke nema dake?". "kina dai kallon yarda nake cikin tashin hankali akan Dr.Karami to ban gaba dawowa hayyacina ba shi kuma Dr.Aqeel ya sako ni gaba da wani lamari wanda ban san ya zan fassara miki shi ba bayan haka ga kuma Huzaif shima ya dauko mani wani tashin hankalin yana kokarin jonawa min a filin rayuwata". "Uhmm ni fa ban gane ba ban san ina kika dosa ba?". Girgiza kai tayi tana jin yarda zuciyarta ke wani irin harbawa da wani tashin hankali mai girman gaske. "Dr.Karami fushi yake yi dani wanda ban san dalilin fushin ba". "wai shin Mariya na tambaye ki mana ke tsakanin ki da Allah zaki ce baki san laifin da kikayi masa ba har yake gudun haduwarku anya kuwa Mariya ya kamata ace kin yi tunani ya kamata ace kin zauna kin yi nazari kin binciko abin da ya haifar da wannan lamarin a tsakaninku". Shiru Mariya tayi kamar mai tunano wani abu na daban kafun ta nisa ta dubi Baseera. "kisan Allah tun ranar da muka fara haduwa dake har period dina ya zo to tun ranar rabona da samun fuska daga Dr.Karami tun ranar muka rabu wanda har yau ban sake sakashi a idona ba". Zaro idanu Baseera tayi tana dafe kirji. "ke Mariya da gaske kike don Allah?". Murmushi Mariya tayi mai ciwo kafun ta gyada kai alamun eh. "Mun shiga Uku anya kuwa Mariya ba wani abu a kasa tsakaninki dashi kuwa?". "Ke ma dai Baseera ta ya ya zan yi wa Dr.Karami wani abu don na bata masa rai ai Alheri bai ce haka ba amma dai ban sani ba ko a cikin RASHIN SANI wanda ake cewa YAFI DARE DUHU nayi masa amma kuma ai ya kamata ace ya nuna min eh ga abin da nayi masa sai in bashi hakuri ba wai ya zauna yana fushi dani ba kuma bai son ganina kin ga kenan abin da nayi masa ba sauki gareshi ba...". "ki daina cewa baya son ganinki Dr.karami yafi kowa a filin duniyar nan son ganinki domin kuwa ni zan yi shaidar haka". Cikin rashin fahimta Mariya take dubanta kafun lokaci guda taji wani lamari ya tunkaro zuciyarta har ya kai cikin kwanyarta da sauri ta mike ta shiga zarya cikin dakin kafun ta tsaya cak! tana tura dan yatsar ta cikin baki tana yawata idanuwanta a sassa na cikin dakin kamar mai son tuno wani abu na daban. "Ya akayi Mariya ko kin tuno wani abu ne na daban". Gyaɗa kai tayi kafun ta dubi Baseera. "Ina zargin wani abu guda domin daga shine koma ya canza tsakanina da Dr.Karami". Da sauri Baseera ta mike jin abin da Mariya take fadi. "zo ki bani labari zo ki sanar dani komai na san za a samu hanyar mafita". Hannunta ta janyo ta zaunar da ita bakin gado tana mai dubanta. "Bani labari Mariya sanar dani komai". Sai da taja numfashi sosai tana jin yarda zuciyarta ke kara matsewa waje daya da wani irin yanayi na damuwa matsananciya. "bana zargin komai sai su Dr.Aqeel da Huzaif domin ranar da muka baro gidanku mun tadda Huzaifa a kofar gidanmu yanayin da naga Dr.Karami ya nuna kamar bai so ba kuma daga lokacin ko kallona bai sake yi ba bayan haka na fito daga motarsa ina kokarin shiga gida sai ga Dr.Aqeel shima ya zo to a wannan lokacin zan iya cewa komai ya faru domin daga lokacin ko kalma daya ba ta sake shiga tsakanina da Dr.Karami ba sosai na tsoro ta da irin kallon da yake mani a lokacin ko dai dai ban san tsananin bacin rai ba amma lokacin na lura da yanayin da ya shiga na bacin rai sosai domin har sai da fuskarsa ta nuna". Hawaye ne suka zubo mata da sauri ta sanya hannu ta na shafe su Baseera ce ta dafa mata kafada tana girgiza kai alamun ya isa haka ta daina zubda hawayen. "Meye tsakaninki da Dr.Karami". Kamar daga sam taji Baseera ta watso mata tambayar wanda hakan ya bata mamaki sosai nan tayi fakare da jajayen idanuwanta tana duban Baseera cikin yanayi na ban gane in da kika dosa ba. "Bakomai". Ta kokarta ta fadi amma tana jin yarda zuciyarta ke karya ta ta akan abin da tace ita a karan kanta ta sani akwai wani abu mai girma tsakanin ta da Dr.Karami amma har zuwa wannan lokacin ba ta san menene ba, ba ta san yarda zata fassara yarda take ji game dashi ba... "Shi kuma Dr.Aqeel fa?". Kamar daga sama ta tsinkayo muryar Baseera ta sake fadi. Sosai ta shiga dubanta a wannan karon tana kallon idanun Baseera da yanayin da fuskarta take nuna alamun maganar da take yi da gaske, ba alamun wani wasa a ciki kan ta shia gyaɗawa kafun ta ja numfashi. "Ban san me zan ce miki ba akan sa, amma dai shima...". "shima ba komai din ko?". Baseera ta katse ta da sauri tana mikewa kan kafafuwanta girgiza kai tashiga yi tana faman sakin yake mai kama da ciwo sosai a zuciya da ruhi take ji, taku biyu zuwa uku tayi kafun ta tsaya waje guda ta juyo ta fuskani Mariya sosai hannayenta sarke a kirjinta kallon sosai tayi mata kafun ta fesar da wata iska mai zafi. "Huzaif fa shi kuma a wani mataki yake a gareki?". Runtse idanu tayi tana mai tallabe kanta da take jin yana dauko mata wani lamari a bangarori duk ukun ba tasan me yake kokarin tarwatsa mata kwanya ba sosai tajin komai na kwance mata tunani ne barkatai taji suna kawo mata farmaki. "Yaa Allah! ban san abin da zana ce dake ba Baseera komai nawa ba ya kan mizanin natsuwa da zan iya warware miki". "Eh dole kice haka mana kuma dole komai ya rikice miki ki kasa gane in da komai na filin duniyar ki ya dosa". Duban ta take yi cikin rashin fahimta sosai ta kasa gane maganganun da Baseera ke yi a hankali taja numfashi kafun ta fesar da iska mai zafi. "Da gaske nake sanar dake ban san komai ba". A hankali Baseera ta tako ta iso gareta kafadarta ta kama ta girgiza sosai idanuwansu suka sarke a juna. "kisan me yake faruwa dake?". Girgiza kai tayi. "Kin san abin da yasa kika shiga wannan matsalar ko ma nace matsaloli?". Nan ma girgiza kai tayi izuwa lokacin jikin ta ya fara sanyi gabanta na tsananta bugawa tana jin yarda zuciyarta ke harbawa da sauri-sauri. Murmushi Baseera ta saki tana mai gyada kai kallo daya zakayi mata ka gane kallon tausayi da rauni take jifan Mariya dashi sai da ta ja numfashi sosai ta fesar kafun ta dauki gorar ruwa ta bulbulawa cikinta zuciyarta taji ta dan sarara da tashin hankalin da take hangowa Mariya a rayuwa ba ta san ta ya zata fara sanar da ita halin da take ciki ba ba ta san ta ya ya zata fahimtar ita ba tare da ta shiga tashin hankali ba ba ma wannan ba sosai take ji a jikinta abin fa ba sauki mutuwar arne. Tana numfasawa zuciyarta na kara mata kwarin gwuiwa akan kawai ta fahimtar da Mariya ita ce hanya daya da take gani komai zai gyaru har a samu mafita. "Mariya ba zan boye miki ba a yarda na fahimci lamarin nan gabadayan wadannan mazajen da kike gani su uku kishi ne a tsakanin su". Wani irin duba na razana Mariya tayi mata tana sauke hannun da Baseera ta daura mata a kafada ta shiga ja da baya a hankali tashiga motsa laɓɓanta. "Ban gane kishi suke yi a tsakanin su ba a akan mi suke kishi". "AKAN SONKI duk kan su son ki suke yi so kuwa mai tsanani ko wanne a tsakanin su akwai kalar so da yake yi miki tun kafun wanann lokacin...". Sulalewar da Mariya tayi ne kasa tare zaman yan bori ya sanya Baseera dubanta tana tsaigaitawa da maganarta ta. Hawaye ne shaɓe-shaɓe ta hanga idanuwan Mariya suna zuba ta hade hannayenta duk waje daya ta daura a kai lokaci guda ta hade jikin ta waje guda kamar mai jin sanyi ko wacce za a rabata da wani abu nata. "Na Shiga uku". Ta fadi tana mai bajewa kan Capet din dake malale tsakar dakin kamar wacce aka tsikara kuma ta mike zumbur tana duban. Baseera da wani irin yanayi. "Ban yarda ba wallahi wannan ba gaskiya bane hauka suke yi wallahi hauka suke yi haba mana Baseera kamar ni za su ce suna so ki dube ni fa guda nawa nake a filin duniyar nan suke kokarin kashe ni da raina wannan wani irin Bala'i uku ne nake ciki ni Mariya". Haka ta saki baki tana sambatu kamar wata zautacciya kafun ta durkushe ta saki wani irin kuka mai zafin gaske da jefa zuciya cikin wani irin raɗaɗi na tashin hankali wanda ba tsammanin yankewarsa. Baseera dake tsaye bata san lokacin da idanunta ita ma suka shiga zubda kwalla ba wani kuka ta ji ya zo mata da sauri ta sanya hannu ta toshe bakin ta tana karasawa wajan Mariya ita ma ta zube nan suka rugumi juna suka shiga rera kuka aka rasa mai rarrashi wani daga cikin su.... *_KAMALA MINNA_*😍😍😍 [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA ASHIRIN DA TAKWAS. A hankali ta turo kofar dakin ta shigo tafiya take yi cikin natsuwa da kuma yanga da ta zame mata jiki da wuya kaga Areefa na tafiya da sauri-sauri a,a sai dai ka ga tafiyar ta kamar mai koyo duk hakan na cikin salo da take amfani dashi cikin filin duniyar rayuwarta sanye take da doguwar Riga Gown wanda tayi matukar amsar jikinta sosai da sosai ta fiddo mata da asalin kyanta da kuma fatarta mai haske wanda tayi Fresh sosai da sosai hutu da jindadi sun taimaka kwarai wajan bayyana a jikin ta kanta ba kallabi sai dai ta tufke gashinta ta sanya rinbos mai kalar pink ta saki jelar gashin na reto a bayan ta fuskar nan fayau ba alamun ko digon tabo na kuraje. Ba ta shafa komai ba natural fatarta kawai ce ke kyalli manyan idanuwanta masu haske sun kara taimakawa waja fiddo da kyan fuskarta hancinta dan madaidaici shi dai ba za a kira shi dogo ba sannan ba za ace dashi gajera ba yana tsaka tsakiya haka bakinta mai dauke da manyan laɓɓa masu kalar ja kadan ba sosai ba suma sun taimaka wajan kara bayyanar da kyan fuskar ta na halinta da Allah yayi mata. A yanayin da ta shigo dakin in ka kalle ta zaka gane akwai abun dake damun ta a filin duniyar rayuwarta bisa yanayin da take yatsine fuska kamar wacce aka sanya dole shan magani sai faman kaɗa idanuwa take yi tana bin dakin da kallo. Hajiya Layla dake zaune can gefe guda tana faman goge jikinta da shawul da alamun wanka ta fito take tsane jikinta. Fuskarta take kallo cikin wani irin yanayi tana yatsine fuska tana duban MADUBI dake tsaye a bangon dakin. Shigowar Areefa ya sanyata tsayawa da abin da take yi ta juyo ta dube ta kafun ta mai da kanta wajan fuskartar madubin. A hankali ta karasa takowa ta iso gareta idanu suka hada ta madubi duk fuskokin su cike da damuwa sosai. "Maama Lafiya kuwa na ga fuskar ki wani iri daban kamar akwai abin dake damun ki ko?". Areefa ta fadi tana mai yawatawa idanuwanta cikin na Hajiya Layla. Numfashi ta ajje mai tauri kafun ta juyo ta dubi Areefa sosai da sosai kafun ta ajje shawul din tana mai riko hannun Areefa tana damkewa cikin nata kamar zata muntsuke sosai Areefa ta ji rikon har sai da ta rintse idanunta tana furta. "Ouchhh!!". Dubanta tayi tana jin zuciyarta na wani irin shiga yanayi sosai take jin rashin dadi a jikinta gabadaya a hankali ta fara motsa laɓɓanta tana son yin magana amma kafun ta kai ga furta kalma daya tari mai karfi ya turnuketa ta shiga yin sa ba k'ank'autawa da sauri Areefa ta ware idanu tana dubanta cikin yanayi na tsoro ta rikota sosai ita ma ta isa da ita daidai karamar kujerar dake gaban Madubin ta zaunar da ita har zuwa lokacin tarin bai lafa ba kwace hannunta tayi daga rikon da tayi mata ta fice daga cikin dakin cikin minti daya ta dawo hannunta rike da glass cup mai dauke da ruwa da sauri ta kai bakin Hajiya Layla wanda a lokacin tari ya tsaigaita sai dai wani lamari da Areefa ta gani ya so tayar mata da hankali domin kuwa wani bakin abu taga yana fita daga bakin Hajiya Layla. "Yaa Rabb!". Ta furta tana mai janyo shawul din tana goge mata baki sannan ta sake mika mata ruwan zuwa bakinta kadan ta sha ta kau da kanta. "Maama meke damunki haka baki da lafiya ne tashi mu tafi asibiti a duba ki mana don Allah kin ji". Yanayin da Areefa take maganar duk a rikice hakan ya sanya Hajiya Layla kakalo murmushi ta ajje a fuskarta duk da raɗaɗin da take jin zuciyarta nayi da wani abu mai girman gaske da ya tokare mata kirji sosai take jin tashin hankali komai take ji na duniyar ya sauya mata ba tun yau ba kusan shekara uku kenan take jin canji a jikinta tayi zayar zuwa asibiti wanda ita a karan kanta ba za ta ce a ga dadi ba sosai ta fara nadamar rayuwar da tayi a shekarun baya sosai take jin daci a zuciyarta dama ruhinta gabadaya nisawa tayi tana mai sake kakalo murmushi tana daurawa a fuskarta domin ta lura Areefa ta shiga tashin hankali matuka ganin yanayin da take ciki wanda ta hakikan ce ba laifin kowa bane sai nata ita ce silar komai da komai a rayuwarta. "Uhmm Ya isa haka Areefa ba komai fa kawai dai tari ne ya tsarke ni magani na sha shine fa tun dazu nake wannan tarin amma yanzu naji komai ya yi sauki ki kwantar da hankalin ki". Rausayar da kai tayi cikin yanayi na sanyin jiki idanuwanta na duban Hajiya Layla da alamun bata gasgata abin da tace ba amma ba zata iya yi mata korafi ba a yarda take kallon ta a matsayin uwa mai kaunar 'yar ta a filin duniyar nan ba za ta mance halaccin Hajiya Layla ba a duniyar ta ba zata taba manta taba domin tayi mata komai na rayuwa ita ce ta sauya mata komai na filin duniyarta a lokcin da ta rasa gata ta rasa wanda zai kula da rayuwarta ya taimaka mata ya ji k'anta a lokacin da ta rasa 'yancita da komai nata a lokacin da take bukatar taimako ta rasa a lokacin Hajiya Layla ta fado rayuwarta tayi mata suttura da taimakon Allah ita ta taimaka mata ta dawo cikakkiyar mace mai 'yanci wacce ba wulakanta ba duk da KETA HADDI da akayi mata aka ci zarafin ta a matsayinta na mace mai rauni a filin a rayuwarta. Bata san hawaye na zuba a fuskarta ba sai da taji hannun Hajiya Layla na dauke mata su da sauri tayi firgigin ta dawo hayyacin ta suka kurawa juna ido kafun Hajiya Layla ta shiga girgiza kai. "Haba mana Areefa har sai yaushe ne idanuwanki za su dai na wahalar da kan su ne har sai yaushe zaki daina zubda hawaye akan abin da ya riga ya wuce bana so ki daina kawai kin ji ko". Gyada kai ta shiga yi kamar wata kankanuwar yarinya kafun ta sanya hannu ta na kara goge fuskarta tana k'akalo yaken dole tana ajjewa a saman fuskarta. Kuri Areefa tayi wa Fuskar Hajiya Layla tana yawatawa da idanuwanta kafun ta nisa. "Maama me ya samu fuskarki haka duk tayi wani iri kamar wacce ta kone da wuta sosai naga ta canza tana tattarewa?". Murmushi tayi wanda ya sanya zuciyarta da ruhinta ciwo sosai wasu HAWAYEN ZUCIYA taji suna ta kwaranyo mata sosai ta san za a yi haka ta san komai daren dadewa sai yanayin nan ya faru da ita wanda ita a karan kan ta ta san ita ce silar faruwar komai a gareta numfashi ta fesar mai zafi kafun ta motsa laɓɓanta. "Ban san ta ya ya zan sanar dake halin da nake ciki ba, ban san ta ya ya zan sanar dake lamarin da na daura wa kai na ba gashi yanzu yana kokarin illa tani ban san mai ya kai ni haka ba ban san mai yasa na kasa godewa Allah da baiwar da yayi mani ba na butulce masa da sani na". Shiru tayi tana jin yarda zuciyarta ke zafi da radadi rufe idanuwanta tayi ta buɗe su akan Areefa da tayi fakare tana kallon ta sosai taji tausayin ta sosai jikinta yayi sanyi da kalaman Hajiya Layla ko da bata ji abin da ya sanya ta shiga damuwa haka ba ta tabbata abin ba mai dadin bane a filin rayuwarta da alamu kuskure tayi ba tare da ta san kuskure bne a rayuwarta. "Areefa kin ga yarda fuskata take a haka cikin rashin kyan gani to haka duk wani sassan jiki na yake". Tana maganar tana janye shawul din dake daure daga kugunta zuwa kasa cinyoyinta ta bude sosai Areefa ta tsorata tana mai runtse idanuwanta kafun ta buɗe su a hankali zuciyarta na wani irin bugawa da sauri-sauri kafar Hajiya Layla take kallo har zuwa cinyarta gabadaya sun sauya kala kamar wanda tayi muguwar k'una ta bada tangarɗa wajan warkewa duk tayi wani bakinkirin ga wasu dikon dikon kuraje marasa kyan gani dago idanunta tayi ta dubi Hajiy Layla dake faman sakin murmushi wanda yafi kuka ciwo. "Maama me ya same ki haka a jiki nace baki da lafiya kin ce a,a ba haka ba ga kuma jikin ki ya nuna alamun baki da lafiya". Areefa ta fadi tana kai hannunta saman fuskar Hajiya Layla tana tabawa cikin yanayi na tsoro a fuskarta runtse idanu tayi jin yarda fatar tayi wani irin tauri da wani giris-giris kamar an shafa mata dakanken gawayi. "Wai meye haka a jikin ki Maama sosai fa jikin ki ya baci fa dubi kafarki ji fuskarki Maam muje asibiti a duba fatarki anya ba cutar fata ba ce ta kama ki?". Girgiza kai kawai take yi cikin matsananciyar nadama da dana sani kafin ta ciji laɓɓanta. "Ba cutar fata bace Areefa ni na sanya wa kai na ba laifin kowa ni na ja wa kaina". Cikin rashin fahimta Areefa ke dubanta tana kara buɗe idanuwanta sosai cikin yanayi na firgici da abin da take ji Hajiya Layla na fadin. "A can baya ni BAKAR MACE ce mutane da yawa suna yabawa na kalar fata ta duk da bakar ce amma ana cewa ina da kalar fata me kyau ba kowa bane ake samu da irin ta Natural skin ce mai wuyar samu domin da wuya ki ga fatar jiki na ta tattare ko ta yi kuraje ni kaina nasan ina da kyan fa sai dai abin takaici abin haushi a lokacin ni kuma ba abin da nake kauna kamar farar fata da yawan kawayena in suka ji ina cewa ina kaunar farar fata sai su ce bani da hankali ban san abu mai kyau ba har cewa suke yi da ana masayar fata dani za suyi ni kuwa a ganina hauka ce kawai suke yi me ake yi da bakar fata ga 'ya mace budurwa mai aji ai bakar fata sai namiji wanda ya gaji wuya da shiga rana ba 'ya mace ba da aka sani 'yar hutu da da zaman jindadi. Duk kururuwar da zuzutawa da akeyi mani ina da kyan fata hakan bai hanani burin canza kalar fata ta ba a lokacin na shiga bincike har sai da na gano irin maya-mayen da ake shafawa ake canza fata zuwa fara a lokacin ba karamin dadi naji a rayuwa ta ba nayi farin ciki mara musaltuwa tun daga wannan lokacin na canza mayuka na da nake amfani da su haka sabulai na duk sai da na canza ban yi sati guda ina amfani da su ba na fara canzawa fuskata ta fara haske a lokacin mutane da yawa sun so nusar dani amma ina na yi kunnan uwar shegu da su na cigaba da harkar ta in takaice miki cikin kankanin lokaci na sauya gabadaya nayi fara tas na koma kamar in kika latsani jini ne zai fito daga jikina sosai na sauya komai nawa ya canza mutane da yawa sun nuna rashin kyautawa akan abin da nayi domin cewa ma suke yi na koma sam bani da kyan gani fatata tada ta fi dacewa dani ni kuwa ko a jikina Areefa na fi shekara goma sha biyar ina wannan abun tun ina kuruciya ta har zuwa tsufana ban daina ba domin ban gano illar haka ba sam sai da shekaruna suka ja fatar jikina ta fara gajiya domin ta rigaya ta gama rauni sosai komai nata ya gama komawa nakashasshe". Shiru tayi tana shafar kafafuwan ta da suka koma kamar mai ciwon kuturta. "Bani da yarda zan yi yanzu domin ni na jawa kaina duk abin da ya faru dani ni ce sila". Ta karasha cikin raunin muryar kafun ta miki ta isa gaban madubi ta janyo robar mai basilin tashiga muttsukawa jikin ta a hankali idanuwanta na kan fatarta tana kallon yarda ta sauya gabadaya kamar wata mai cutar kuturta nisawa tayi ta dubi Areefa da tayi fakare tana bin ta da kallon ko motsi ta kasa yi. "Yau ba zaki aiki bane hala lokaci fa na tafiya". Sai lokacin Areefa ta kaɗa idanuwanta tana mai jan numfashi ta bude idanunta sosai ga Hajiya Layla wani irin tausayinta take ji yana samun masauki a zuciyarta da ko ina na gangar jikinta girgiza kai ta shiga yi alamun ba za ta je ba domin yanayin da take jin jikin ta duk yayi sanyi kalaman Hajiya Layla ba karamin sanya zuciyarta rauni sukayi ba. Ware idanu Hajiya Layla tayi ganin abin da Areefa tayi kallonta tayi tana ma tsuke fuska. "Maza wuce ki shirya ki tafi aiki kin ji ko akan me zaki ce ba zaki ba ke da ba wani abu ke damun ki ba". kau da kai tayi tana kokarin yin magana Hajiya Layla ta daga mata hannu. "Bana bukatar naji komai kawai ki tafi nace ki shirya ki wuce Office". Ba ta sake yin magana ba gani ba wasa a fuskar Hajiya Layla din cikin sanyi jiki ta ja jiki ta fice daga daga dakin. Kamar jira take yi Areefa ta fice ta zube kan gado gami da zabga uban tagumi tana mai runtse idanuwanta sosai taji kanta na sara mata zuciyarta na zafi da wani irin yanayi mai girman gaske nadama sosai take yi tana jin kunyar kanta fita ma waje kunya take ji ba ta so su hadu da muta ne gani take yi kamar kallon banza da kallon kyama suke yi mata. ******* A hankali ta karasa shigowa cikin harabar Company din can gefe inda aka tanada Parking Space ta isa ta ajje motarta sai da ta shafe mintina kafun ta fito daga cikin motar hannun ta rike da Key sai jaka kunnanta kuwa iyafis ta mak'ala fuskar ta kawai zaka kalla ka gane akwai damuwa tattare da ita. A hankali ta fara taku lokaci-lokaci tana lumshe idanuwanta har ta isa babbar kofar da za ta shigar da ita cikin wajan aikin nata Securty suna yi mata sannu da zuwa amma ina hankalin ta yayi dogon zango. Ko da ta isa ciki ba wanda ta tsaya kallo har ta isa wajan gefen ta ta buɗe yar karamar kofar da kayi domin kare wajan zaman nata ta buɗe ta shiga ta zauna tana sakin numfashi kadan-kadan table din dake dauke da computer da file ta duba kafun ta janye files din da taga an anje mata gefe kanta ta daura akai tana tallabewa da hannayen ta zuciyarta take ji tana tayi mata wani irin sosai take jin rashin dadi a jikin sosai komai taki ji nata ya sauya yau daya wani irin kunci da zafin zuciya take ji sam bata so wani ya zo ya takura mata shiyasa bata so fitowa aiki ba amma ba yarda za tayi ne shiyasa... Kwakwasa mata kofa da akayi ne ya sanya ta dago kai tana mai sakin guntun tsaki Sakatariyar Dr.Erena ce tsaye sai faman wani shan kamshi take yi tana harare harare kamar wacce ke kokarin kai duka. "Sir ya ce sai ki zo". Ta fadi tana wani basarwa kamar ba da Areefa take yi ba. Sosai Areefa ta ware ido tana kallon ikon Allah wai suruka ta mari uwar miji ita abin ma dariya ya so ya bata wai batar basira rokon Allah da goge sai da ta gama kalle ta kafun ta ja wani dogon tsaki tana mai da kan ta kasa ta na kwanciya. kwankwasawa taji an sake yi da sauri ta dago cikin bacin rai ta mike kan kafafuwan ta tana dubanta. "Ke! ina wasa dake ne ko ni tsaran ki ce ba sako aka baki ba kin fadi ba sai ki tafi ba ko da sauran wani abu ne?". Areefa ta fadi cikin daga muryar har sai da sauran ma'aikatar hankalin su ya yo kan Areefa da sauri ta fizgi wayar ta ta fito ta tsaya gabanta tana watsa mata wani irin kallo kafun ta ja wani tsaki ta wuce abin ta. ta bar ta shanye da baki cikin yanayi na tsoro don bata taba tunanin Areefa haka take ba tun da ta fara aiki a Company din ba tayi zaton tana da fada haka ba ashe kallon kitse take yi wa rogo kwaɓe baki tayi kafun ta ja jiki ta bar wajan tana duban Sauran ma'aikatan da suka kureta da ido kamar za su lashe duk sai taji kunya ta kamata. Ko da Areefa ta isa Office din Dr.Erena banka kofar tayi ta shiga cike da bacin rai tsaye ta hangeshi sai faman safa da marwa yake yi jin banko kofar da akayi ne yayi sauri tsaya cak! Yana duban kofar ganin Areefa ya sanya shi ware idanu musamman ganin yarda ta shigo kamar wacce zata rufe shi da duka. "Dr.Erena ya kamata ka san wani abu ba wai don ina karkashin ka bane ina aiki zai baiwa sakatariyarka dama wani duk da yake cikin ma'aikatar nan raina ni ba fa maula na zo yi ba aiki na zo yi kamar kowa da yake tutiyar aiki ya zo yi don haka ba wanda ya isa ya taka ni na kyale shi". Ta karashe tana fesar da iska mai zafi shi kan sa sai da ya razana da yanayin ta da sauri ya iso gareta jikin sa har rawa yakeyi. "Lafiya me aka yi miki wani dan iskar ne ya bata miki rai a cikin Company nan nawa?". Yanayin da yake maganar cikin yanayi na harzuka ya sanya Areefa duban sa cike da mamaki kafun ta kau da fuska. "kar ka sake tura mani sakatariyarka in kana nema na ai akwai waya ko ka kira ni mana". Tun kafun ta dire maganar ta taga ya figi jikin sa yayi kofar fita kofar ya banka cikin sauri ya fara kiran sunan sakatariyarsa wacce a daidai lokacin ta iso tana kokarin zama amma jin kiran da Ogan nata yake yi mata ya sanyata sauri mikewa tana rarraba ido kamar wacce ta san bata da gaskiya. Yana isa gareta ya nuna ta da hannu kafun ya kwasheta da mari ji kake tas! wata kara ta saki gami da kiran 'jesus'. saura kadan ta hantsila bayan kujera nan ta shiga ja da baya idanuwanta a warwaje ganin yanayin da yake nunata da yatsa cikin matsanancin bacin rai. "Sorry Sir...". Wata mahaukaciyar tsawa ya daka mata kafun ya fara magana cikin masifa. "Baki da hankali uban me tayi miki zaki nemi raina mata wayo dana aike ki cewa nayi ki yi mata rashin mutunci ba cewa nayi kawai ki duba in ta zo ki ce ina kiranta ba da yake ke dakikiya ce shine kika je kina yi mata hauka ko". ware idanu tayi tana duban hanyar Office din sa da wani irin yanayi na dacin rai a ranta tana sa ba wanda zai mata haka sai Areefa tun da suke da Dr.Erena bai taba ko zaginta ba amma yau ta dalilin ta ya mare ta dubansa tayi cike da takaici kafun ta kau da fuskarta zuciyarta na yi mata zafi ba abin da take yi a zuciyarta sai 'Allah ya isa ba ta yafe ba' Wani mugun kallo tabi shi dashi lokacin da ta ga ya ja tsaki ya koma office din itama dogon tsaki ta ja zuciyarta kamar ta fashe janyo kujera tayi cikin takaici ta zauna tana dukan saman table din dake gabanta. Shikuwa Dr.Erena yana shiga Office dinsa zaune ya tadda Areefa sai faman girgiza kafa takeyi fuskar nan ta ta kamar hadari ba karamar razana yayi ba da sauri ya isa wajan yana mai bata hakuri yana kokarin zama kusa da ita tayi saurin jan jikin ta tana wurga masa wani wulakataccen kallon. "Don Allah Areefa kiyi hakuri waccen tsinaniyar yarinyar ba hankali gareta ba shiyasa don Allah karki bata ran ki akan ta na hukunta ta". Kallo shekeke tayi masa gami da na raina maka wayo kafun ta ja guntun tsaki tana kokarin tsahi ta fice da sauri ya sha gabanta yana kallon idanuwanta da wani irin yanayi na tsananin so da yake yi mata. "Haba mana magana fa zamuyi shiyasa nace a kira mani ke don Allah koma ki zauna maganar ba za ta yuwuwa ba a tsaye". "ka ga don Allah Dr.Erena ka rabu dani bana bukatar yawan magana a daidai wannan lokaci ina bukatar zaman kadaici ni kadai please". "Areefa don Allah ko mintin biyu ki bani wallahi maganar mai muhimmanci ce". Duban sa tayi ba tare da ta ce dashi komai ba ta koma ta zauna hakan da ya gani shima yayi saurin jan kujera ya zauna yana fuskartanta sai faman ajiya numfashi yake yi kafun ya kokarta duban idanunta sosai da sosai. "Areefa ba zan boye miki ba a gaskiya nagaji da yanayin da kike yi mani na shariya da halin-ko-in- kula ya kamata in san matsayina domin ni dai da gaske son ki nake yi kuma ko auren ki zan iya yi...". wata irin zabura tayi ta mike kan kafafuwan ta kafun ta lailayo wasu tawagar ashariya ta sauke ta dora da fadin. "Kan Uban can! So Aure fa ka ce Dr.Erena wa zaka aura". Ta fadi tana mai sakin wani murmushi mai kokarin tarwatsa mata zuciya da ruhi wani daci ne gami da raɗaɗi taji sun saukar mata a zuciya kirjinta yana wani irin bugawa kamar zai tarwatse lokaci guda taji kwanyarta tayi wani irin hautsinewa kamar zata tarwatse itama duban sa take yi da wani irin yanayi na tsana mai girman gaske idanuwanta lokaci guda suka sauya fuskarta tashiga wani kunci runtse idanuwan ta tayi kafun ta sake dubansa ta girgiza kai da sauri ta ja kafarta tayi hanyar ficewa daga cikin office din cike da tashin hankali da a zuciya kiranta ya shiga yi amma ina ko ta kan sa ba tabi ba illa banka kofar da tayi har sai da office din gabadaya ya amsa da sauti mai girman gaske. Da gudu ta isa kasa ba ta tsaya wata wata ba ta fizgo jakarta ta fice daga cikin wajan da yawan ma'aikata kallo suka bita dashi har fa fice wajan motarta ta isa ta buɗe ta shige tana mai da numfashi kai ta hada da sitiyarin motar gabanta na wani irin dokawa tsanar Dr.Erena take ji tana kara samun filin zama a zuciyarta ko son ganin sa ba ta so ta sake yi ta lura da gaske yake yi kokari yake yi ya gama da ita tun kafun ta cika burin ta akan sa wanda ba zata so hakan ba sam!. Ya zame mata dole ta canza taku dole na biyo masa ta hanya wacce zata yi saurin cimma kudirin ta domin a gaskiya ta gaji da zuwa wajan gani take yi kamar komai zai lalace yar da ta fuskanci al'amarin Dr.Erena so yake yi yayi mata yawo da hankali wanda ba za ta yarda haka ta kasance ba dole ta sake sabon lale tun wuri.... *_KAMALA MINNA_*😍😍😍 UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA ASHIRIN DA TARA. Cikin wani irin yanayi ta kai wayar kunnan ta sai faman jan numfashi take yi daƙyar idanuwanta sun kada sunyi jajir kamar an watsa mata barkono zuciyarta take ji tana mikata cikin wani irin waje mai dauke da tashin hankali mai girman gaske komai take ji ya tsaya mata cak! ji take yi kamar motar ta ta tuntsiran da ita ta mace ko ta huta da wannan tashin hankalin da kunar da zuciyarta ke yi tana babbaka duk wani sashi na kirjin ta ruhinta take ji yana wani irin fizga mai haifar mata da wani matsanan cin ciwo a dukkan sassan jikinta. Girgiza kai take yi tana jin yarda yake wani irin sarawa da duk tashin hankalin da take ciki komai take ji a wannan lokacin yana barazana da duk ragowar farincikin da yayi sauya a gareta na filin duniyarta. Ba ta san abin da ya sa ta fito yau ba bata san mai alkalamin ƙaddararta yake kokarin rubuto mata ba sosai take jin zuciyarta na haifar da wani kunci mai radadin gaske sosai take jin duk wani sashi na jikinta yake narkewa kamar ba na ta ba kafafuwan da suke kan giyoyin motar take jin su kamar ba a jikin ta suke ba ta tabbata da a tsaye take ba za su iya daukar gangar jikinta ba. Nisawa tayi a daidai lokacin da taji iska mai nuna alamun an daga wayarta ta buso cikin kunnuwan ta runtse idanu tayi gami da tura laɓɓanta gabadaya cikin bakinta tana cizawa kamar zata fizgesu daga mazauninsu. A hankali ta fara gangarawa gefen titin domin ba zata iya furta ko da kalma daya a yarda take jin zuciyarta ba, ba za iya motsa wani sashi na laɓɓanta a cikin halin tuki ba ji take yi kamar in ta motsa su komai zai tarwatse a gareta. Sai da ta shafe mintina biyu kafun ta ja wani dogon numfashi ta fesar mai matukar ciwo. "Alhaji Abdulwahaab". Ta fadi can kasar makoshin ta kamar wacce akayi wa dole sai ta ambaci sunan. "Na'am Areefa". Ya ansa da yanayi na farinciki a muryarsa. Runtse idanu tayi kafun ta sake jan numfashi. "Kana ina Please I need your help right now?". Yanayin da take furta kalmar cikin sauti mai rauni ya sanya Alhaji Abdulwahaab yin sanyi sosai. "What is wrong with you Areefa me ke faruwa dake ne naji muryar ki So Sad?". "Kana ina right now Alhaji Abdulwahaab don Allah ina son ganin ka ko a ina kake ka fada min gani nan zuwa". Sosai muryarta tayi rauni kamar zata fashe da kuka a hankali ta kai hannunta baki tana toshewa. "Ok...Cool down Please yanzu haka ina Muhabbir Coffee daidai Alo-Vera Hotel ki zo nan ki same ni". Ba ta ji ra abin da zai ce ba da sauri ta sauke wayar tana cilli da ita kan kujerar dake gefen ta wani wawan ribas tayi tare da juya akalar motar ta koma kan titin sosai ta hau hanya. Zabga gudu take yi kamar wacce zata tashi sama ita akaran kanta ba ta san ta nayin sa ba zuciya ce kawai ke aikinta domin ba ta cikin hayyacita motoci da yawa sai dai su kauce mata domin sun lura ba ta cikin hayyacin ta cikin mintina kalilan ta hau titin da zai kai ta alo-vera Hotel kwanar da zata sha saitin W. I .WUSHISHI ESTATE. Sukayi a rangama da wata motar saura kadan su haye juna Allah ya tsagaita amma duk da hakan ta bugar wa mai motar fitilu har sun dan tsage hannu kawai ta daga masa alamun bashi hakuri ta shiga layin girgiza kai yayi mai motar don ya lura bata cikin hayyacin ta. Tun kafun ta isa Muhabbir Coffee din tayo parking din motarta gefe guda ta fito cikin hanzari murfin motar ma da kafarta ta tura ta shiga sauri kamar zata kifa har tana turgudewa Allah ya taimaka bata je kasa ba. Ta shiga Get din wajan ta shiga rarraba idanu can gefe guda ta hango shi yana dago mata hannu kamar wacce aka ingiza haka ta tafi tana isa ta tsaya kinkam! A tsaye tana mai da numfashi ta shiga nuna kanta da hannu kirjinta sai faman dagawa yake yi idanuwanta na juyawa kamar mai shirin zubewa a kasa da sauri Alhaji Abdulwahaab ya mike don ya lura bata cikin hayyacinta jakarta ya riko ya ajje kan Table din dake wajan kafun ya riko hannunta ya zauna da ita sosai gorar ruwan dake ajje a wajan ya murɗewa kai ya tsiyaya cikin Glass Cup ya mika mata kau da kai tayi cikin wani irin yanayi. "Haba mana anshi ki sha ko kya samu sa'ida a zuciyarki". "Bana tunanin ruwa zan yi mani wani amfani a halin da nake ciki a yanzu". Ta fadi cikin wani irin yanayi tana daura hannayenta saman goshinta da take ji kamar zai dare gida biyƴ. "Ki ansa ki sha Areefa ruwa zai miki abin da baki taba zato ba". Ba ta bukatar surutu da yawa don haka ta anshi ruwan ta kai bakinta aiko sai gashi ta take ruwan gabadaya ta dire kofin da karfi har sai da ya tsage don wahala runtse idanuwanta tayi tana faman sauke ajiyar zuciya a hankali gumi ya karyo mata saman goshi idanuwanta a lumshe sosai taji wani sashi na zuciyarta da ruhinta sun yi sanyi kadan da ta sha ruwan. Lokaci guda ta ware idanuwanta kan na Alhaji Abdulwahaab da yayi kuri yana dubanta nisawa tayi cikin fesar da wani zazzafan huci. "Wai ni Dr.Erena yake so har yana ikirarin zai aure ni". Ta fadi tana runtse idanuwanta zuciyarta take ji tana kartawa da wani irin tashin hankali mai girma wata irin tsana mai tsanani da take ji akan Dr.Erena take samun fili a zuciyarta tana kara hauhawa sosai take jin kalamansa na ansa kuwwa a kwanyarta da zuciyarta. Da na sani take yi na zuwan Company yau da na sani take yi da har ta je Office din sa ta saurare shi dana sani take yi da har ta bari kunnuwanta su ka jiyo mata kalaman da suke kokarin tarwatsa mata zuciya. Wasu hawaye ne masu tsananin dumi taji suna biyo fuskarta da sauri ta ware ido tana kai hannayenta tana taba su murmushi take saki mai tsananin ciwo kafun ta dubi Alhaji Abdulwahaab mamaki fal a zuciyarta da fuskarta murmushi taga yanayi har hakoransa na bayyana kafun ya mike kan kafafuwansa yana taku a hankali hannayensa goye a bayan sa. Juyowa yayi ya dubi Areefa har lokacin murmushin bai kau ba sai ma kara fadada da ya yi dawo wa yayi ya zauna sosai yana daura kafa daya kan daya ya jawo Mug din Coffee yana kaiwa bakin sa da wani irin yanayi na nishadi sai da ya kurba sosai sannan ya dire ya daura hannunsa kan Table din yana dan kwankwasawa har zuwa lokacin idanuwansa na kan Areefa da tayi fakare tana dubansa a wani irin yanayi mai cike da mamaki da AL'AJABI mai girma gaske wanda ya kusan sanya zuciyarta tsalle sama. "wondefull Story". Ya fadi yana mai girgiza kai cike da farin ciki kafun ya dora da fadin. "Sosai da sosai naji dadin wannan ranar a daidai wannan lokacin da na samu daddadar lamari irin wannan How Comes na ce miki yau ce ranar farko da nake hango cinmma nasarata akan Dr.Erena". Mikewa ya kuma yi kan kafafuwansa hannunsa rike da Mug din Coffee. "Areefa ya kamata ace wannan lamarin ya samu nishadi a filin duniyar rayuwarki a yanzu...". "Alhaji Abdulwahaabbb!!". Areefa ta fadi cikin wani irin sauti mai haifar da ɗaci a saman zuciya tana mikewa kam kafafuwanta idanuwanta a warwaje tana dubansa ciki da kunci zuciyarta na wani irin zafi. "Ban san mai yasa kake farin ciki da haka ba, Ban san mai yasa kake so nayi farin ciki da wannan lamarin ba, shin ka mance abin da ke tsakanani da Dr.Erena, shin ka mance abin da yasa na ke zaune a INUWA DAYA tare dashi, shin ka mance bani da makiyi a filin duniyar nan sam dashi, shin ka manta ba wanda na tsana duniyar nan na ke son na ga bayansa sama da Dr.Erena". Runtse idanu tayi tana jan numfshi kafun ta ciji laɓɓanta tana dakune fuska. "Alhaji Abdulwahaab ta ya ya ke zaton zan yi farin ciki, ta ya ya kake zaton ko hakorana zan bayyana a fili a dalilin wannan maganar haba mana Alhaji Abdulwahaab kayi tunani mana". Ta karashe tana komawa saman kujera ta zauna hannayenta dukka biyu ta dafe kanta dasu wani irin yanayi take jin zuciyarta na haifa mata wanda take jinsa kamar kirjinta zai kama da wuta ya babbake duk wata halitta dake da gurbi a filin kirjin nata ba ta san mai yasa ma ta zo wajan Alhaji Abdulwahaab ba tayi tunani zai ce da ita wani abu akan wannan lamarin ba amma sai taga sabanin haka wai farin ciki yake yi har ma da dariya. "Yaa Salam". Ta fadi tana saukar da hannunta daya tana dafe kirjinta dake ji yayi mata wani irin nauyi mai girman gaske. "AREEFA!". Alhaji Abdulwahaab ya fadi da murya mai zurfi. Dago kai tayi ba tare da ta ansa shi ba illa ido da ta zuba masa. "Wannan lamarin da ya faru nasara ce a tsakanin ni da ke". Kau da fuskarta tayi jin zuciyarta na kara rura wutar zafin da take ji. "Nasan zaki ji ba dadi amma wannan hanyar ita ce ta dace ki bi don cimma kudirin ki har ma da nawa". Girgiza kai ta shiga yi tana yatsine fuska kafun ta mike kan kafafuwanta tana dubansa. "Ina! wannan ba hanyar mafita bace Alhaji Abdulwahaab bana hango nasara ta a wannan hanyar". "Don ya furta ya na son ki ko shine kike wa kallon rashin nasara?". Ta gaji da sauraron kalaman sa domin ranta ya fara baci ba za ta iya cigaba da zama ta na sauraronsa ba. Hannu ta saka ta janyo jakarta kafun ta dube shi. "Tafiya zan yi nayi tunanin in na zo maka da maganar nan zan samu mafita a gareka domin cimma burinmu da KUDIRI ashe ba haka bane". Ta karashe tana takawa kan kafafuwanta. "Areefa". Ya fadi yana mikewa da sauri ya isa gabanta yanayin sa ya sauya sosai yake jin tausayin Areefa sai dai wani abu guda yake hango wanda wannan hanyar ce kawai da suka samu ita ce dama da ya kamata ace sunyi amfani da ita kar su sake ta kubace musu. "ki tuna Areefa kudina ya ansa da sunan muyi haɗaka wajan bude Company kudin da bana wa ba kudin Marayu wanda sam bani da hakki a cikin su kudin da suke zama masifa ga duk wanda ya cisu ya kamata ki tuna ba yarda za ayi na so bayar da gudun mawa ya cutar dake nima ina bukatar naga Dr. Erena ya shiga tashin hankali ina so naga Dr.Erena ya fada cikin halin masifa domin ba mutum bane mai tausayi ba mutum bane mai imani jahadi zakiyi sosai yaci zarafin mutane da ba su ji ba su gani ba sosai ya zalunci mutane wanda na tabbata har dake a ciki. AL'UMMA zaki taimakawa jama'a duniyar na zaki ceto daga fadawa komarsa damarki ce wannan lokacin ki ne wannan Areefa kiyi amfani da ita nasara na tare dake mutane da yawa za su shi miki albarka za suyi miki fata nagari za suyi miki addu'a ki gama da duniya lafiya na rokeki ke kadai ce zaki iya wannan aikin". Komawa yayi ya zauna yana mai ajjiyar zuciya tausayin Areefa yake ji sosai a ransa ya sani dole taji ba dadi a ranta dole tashiga wani hali na tashin hankali Amma kuma jahadi za tayi taimakon mutane za tayi ya sani Dr.Erena yana da hatsari Areefa kawai zata iya yin komai in tayi taka tsantsan ba tare da ya gano ta ba musamman yanzu da ya nuna yana sonta ya sani sosai hankalinsa zai karka akanta da komai na shi ya sani Dr.Erena bai iya son abu ba yana nuna maitarsa a fili kuma yana bi ko ta halin k'ak'a ne don ganin ya cimma burinsa akan abin da yake so. Areefa da ta kasa tafiya tun lokacin da Alhaji Abdulwahaab ya fara bayaninsa gabadaya jikinta yayi sanyi sosai taji zuciyarta narkewa da wani irin rauni mai girma a hankali ta juyo ta dube shi kafun ta gyada masa kai shima kai ya gyada mata don bai gane in da ta dosa ba. A hankali ta juya ta fara tafiya a jiki a sanyaye zuciyarta na shiga wani iri yanayi tana cakuda maganganun Alhaji Abdulwahaab a zuciyarta da kwakwalwarta har ta fice daga wajan ta isa inda ta ajje motarta tashiga sai da ta shafe mintina kanta akan sitiyari domin komai take ji ya tsaya mata cak! gabadaya taji duniyar tayi mata wani gin-girin-gim kafun ta yi wa Motar Key ta falle kan titi. ******* A hankali ta turo kofar falon idanuwanta a rufe kadan saboda raɗaɗin da taji sunayi mata kamar jijiyoyin su zasu tsintsinke haka ta zuro kafa cikin falon tana mai ware idanuwanta baki daya tana kokarin gayyato natsuwa ko ya ya ne bata so Hajiya Layla ta san tashin hankalin da tashiga sosai da sosai bata so ta gane tayi kuka da idanuwanta bata so ta saka ita ma cikin tashin hankali don ta tabbata itama akwai abin da ke damun filin rayuwarta. Nisawa take yi a hankali zuciyarta na kara matsewa wani irin yanayi mai girman gaske idanuwanta ta sauke a inda take tsammanin samunta kamar ko yaushe da ta maida wajan zaunin ta har in ita ba ta nan. Hango tayi zaune ta zabga tagumi da hannu daya hannu guda m Kuma rike yake da wani kwali wanda bata gama hakikance na mane ne ba amma zuciyarta ta buga lokacin da taga Hajiya Layla ta kura masa idanuwa ko kaftawa bata yi. Kara ware idanuwa tayi tana fiddo su kamar wacce zata barsu su faɗo kasa nisawa take yi da wani irin yanayi ganin kwalin dake hannunta sosai ta tsorata tana sakin jakar dake hannunta tana faduwa kasa ba tare da ta sani ba kafafuwanta taji sun shiga rawa kamar za su kasa daukar gangar jikinta da sauri ta fara taku tana haɗe hanya har ta isa gareta ba tare da ta sani ba. Hannu ta kai ta ansa kwalin cikin wani irin yanayi mai nuna alamun mamaki matuka gaya idanuwanta take yawatawa kan kwalin ba tare da tace kazil ba ta shiga bin Hajiya Layla da kallo wacce ita ma ansar kwalin da Areefa da tayi a hannunta shi ya dawo da ita hayyacinta ta shiga duban Areefa a daidai lokacin kwalla masu yawan gaske wanda suka jima tare a idanuwanta suka zubo ta shiga girgiza kai. "Maama". Areefa ta fadi da muryarta mai zurfi idanuwanta da tuhuma acikin su take dubanta tana mai gyada kai tana jin yarda zuciyarta ke kara matsewa da mamakin da bata yi zaton taddashi a gidan ba. "Dama Da...ma ba ki dai...na baaa!". Ta sake fadi muryarta na rawa kalmomin da take fadi suna rarrabuwa da junansu. Wani kuka ne ya kufcewa Hajiya Layla hannu ta saka ta toshe bakin ta kafun ta shiga girgiza kai. "A,a Areefa wallahi na daina ban sha yanzu kwata-kwata ko kaunar ta bana yi kisan nayi miki alkawari har gaban abada ba zan sake ba". Girgiza kai Areefa ta shiga yi tana mai zubewa a wajan numfashi take ja dakyar zuciyarta na wani irin zafi da radadi kafun ta fesar da wani zazzafan huci. "Haba mana Maama sau nawa za muyi maganar nan dake na fada miki illar wannan abun likitoci ma sun fada miki wanda suke k'irk'irarta ma sunyi nuni da cewa tana da illa ga rayuwar duk mai ta'amali da ita ya kamata ki san wannan ya kamata ki duba halin da kike ciki ya kamata ace kin ceto sauran rayuwarki da tayi saura a filin duniyar nan kina ji likita ya fadi ta fara baki matsala sosai wanda yace in ba daina wa kikayi ba to tabbas nan da dan lokaci kadan zaki rasa rayuwarki gabadaya ni kuma ba zan so haka ba Maama AKWAI ILLA a rayuwar shan taba tana da matukar hatsari ga duk mai rayuwa da ita kin sani kuma kinji a jikinki lokacin da kika kwanta rashin lafiya kin ga yanayin da kika shiga na tashin hankali da kyar da taimakon Allah ki ka samu kan ki sosai likitoci suka nuna miki dokoki da zaki bi sannan kiyi kokarin fidda sha'awarta a rayuwarki ko ganinta ki nisanta daga rayuwarki haba mana Maama me yasa haka me ya kawo kwallin taba cikin nan gidan?". Areefa ta karashe cikin muryar rawa da son fashewa da kuka tasowa tayi ta iso gareta ta kama hannayenta ta rike su gam!. Tana mai a jiyar zuciya laɓɓanta take tura cikin bakinta tana cizawa a hankali. "Me ya kawo kwallin sigari nan gidan Maama?". Ta sake fadi idanuwanta na kawo kwalla kafun ta rintse idanu. "Nayi dana sani a rayuwa ta nayi tir da rayuwar da nayi a duniyata duk a dalilin rashin 'yanci yau na ga illar rashin iyaye yau na ga illar haihuwata da kayi a titi ban san me nayi wa iyayena ba suka yasar dani suka tafi suka bar ni a titin Allah ban san mai yasa sukayi mani haka ba yanzu ga shi nan na rayuwa cikin rashin amfani na tashi cikin rashin 'yanci na rasa mai kwaɓata na rasa mai kula min da rayuwa har ya nuna min kuskure na rayuwata gabadaya ba tayi amfani a duniyar nan ba ni ban yi aure ba balle na samu zuri'ar da za su ji k'ai na ni ban yi rayuwar yanci ba rayuwar titi nayi wacce ba zan ce miki ga yarda na kasance a rayuwata a shekarun yarinta ta ba". Nisawa tayi wasu hawaye suka zubo mata kafun ta cigaba da fadin. "kawai na yi rayuwa ce a yarda ta zo mani a yarda Alkalamin kaddara ya zana min wani fannin kuma da nawa kason na lalacewar rayuwata ban san dadin iyaye ba ban san su waye iyaye ba ban san ya yaro yake ji a wajan iyayen sa ba ban san wacce irin kauna ce da ake fadi ana ji a wajan UWA DA UBA ba iyayena sun kasance ne bakin titi da wajan masu abincin saidawa nan ne suka kasance jigon rayuwa ta su ne suka kasance iyaye a gareni har lokacin da na dauki kazamar rayuwa da nake zaton ita ce mafita a gareni na daura a duniya ta". runtse idanu tayi tana jin yarda kirjinta ke harbawa da duk wani ɗaci gami da zafi a ranta. "Areefa na daina shan sigari tun da nayi miki alkawari yau ma fita nayi aka zageni aka tsine mani har ake kokarin marina akan sigari wai don kawai nace na daina yaro karami wanda in a haife ne na haife shi in jika ne ma zan iyayi dashi amma akan abin banza abin Allah wadai ya zage ni yana jifana da kwalin sigari dake hannunsa Yaa Allah wannan wacce irin rayuwa ce Areefa nayi dana sanin rayuwa a duniyar nan". Wata irin zabura tayi idanuwanta a warwaje hannayenta saman kirjinta. "Maama zagi fa kika ce waye ya zage ki fada min waye shi na nuna masa ke ma kina da gata a rayuwarki rashin iyaye ba hauka bane zan nuna masa kina da gata kuma kina da 'ya a filin duniyar nan da ta san darajar ki da kimarki ki fada min shi please Maama". Cikin sauti take maganar kamar wacce ta fice daga hayyacin ta da sauri Hajiya Layla ta mike ganin Areefa na kokarin ficewa daga gidan sosai ta rikota ta zauna da ita tana mai kwantar da ita a jikinta tashiga shafa mata baya a hankali har zuwa lokacin idanuwanta na zubda hawaye masu tsananin zafi da take ji kamar za su keta mata duk wani sashi na kirjinta. "ki bar komai na yafe masa rayuwa ce ta zo da haka inda ban yi harkar shan sigari ba ba yarda za ayi ya tare ni a hanya har ya ci mani mutunci in ba don ya ga alamun nayi shaye shaye ba a zamani na ba yarda za ayi ya dube ni yace na bashi sigari komai ya faru ni ce sanadi ni ce sila Areefa ki bar komai na yafe masa". Da sauri ta dago kanta tana duban Hajiya Layla da take shafe hawaye. "Haba mana Maama hawaye fa ya sakaki zubdawa akan mi zaki ce a bar shi bayan ya ci miki mutunci". "ki bar shi nace kawai ki bar shi komai ya wuce a wajena har a zuciyata na yafe masa fata na Allah ya shirye shi ya sa daga kaina ya daina abin da yake yi domin na lura illar shaye-shaye yawa gareta ba abin da ba zata iya sanya wa ka aikata ba wanda zai cutar da rayuwarka sosai AKWAI ILLA sosai da sosai". Ta karashe tana mai kalato murmushi tana daurawa a fuskarta domin kwantarwa da Areefa hankali domin bata so ta sake sanya rayuwarta a damuwa nan ta shiga bubbuga bayanta domin kwantar mata da hankali. Wani numfashi a Areefa taja mai tsayi kafin ta saki ajiyar zuciya. "Maama ke dama baki da iyaye dama ke ma marainiya ce kamar ni". "Ya isa haka Areefa mu bar wannan zance haka ba shi da amfani". Ta katse ta da wani irin yanayi da ta ji zuciyarta na shiga da tashin hankali mai girma. "Mai ya dawo dake wannan lokacin ba tare da lokacin tashi ya yi?". Ta fadi domin kau da zancen da Areefa ta dauko. Da sauri ta tashi zaune tana duban idanun Hajiya Layla kafun taji wata irin tsanar Dr.Erena ta sake samun fili mai girma a zuciyarta a hankali ta shiga cizon laɓɓanta tana runtse idanu. "Dr.Erena Maama". Ware idanu tayi kafun ta mike tsaye tana kai kawo a tsakar falon lokaci guda ta tsaya cak! fuskarta ta kara cakuɗewa da bacin rai mai girman gaske. "Ba dai kin yi sake ya gano ke wa ce ce ba in kuwa haka ne komai zai wargaje mana". "A,a Maama wai cewa yayi yana sona har cewa yayi zai iya aure na in har na yarda dashi". Zare idanu tayi waje bakin ta na buɗe ta iso ta zauna tana janyo Areefa jikinta gami da sarke hannayensu waje guda wani murmushi na takaici ta sako kafun ta dubi Areefa sosai da tayi fakare tana dubanta ganin abin da ke fuskarta. "Lokaci ya zo Areefa lokacin da nake dako ne Allah ya kawo mana shi tabbas lokaci ne ya zo tsakanimu da Dr.Erena". "Ban gane ba Maama?". Areefa ta fadi a dan tsora ce tana kwace hannayenta daga cikin na Hajiya Layla. "Karki damu kawai ke dai ki kwantar da hankalin ki ki cigaba da zuwa aiki karki sake ko da wasa ki nuna masa baki amince ba sannan gobe karki sake ki ce ba zaki office ba ki shirya ki je ki bar komai a hannu na". Cikin rashin fahimta da kara bayyanuwar mamaki ta shiga motsa laɓɓanta tana kokarin yin magana amma Hajiya Layla ta hana ta tana mai cewa. "Maza ta shi ki je ki watsa ruwa ki ci abinci ki huta kafin lokacin Sallah yayi". Ba musu ta mike zuciyarta da wani irin AL'AMARI wanda ta kasa gane kansa sosai kanta ya kulle sosai taji tunanin ta ya kasa buɗe mata wannan lamari wanda ya jefata a duhu sosai da sosai haka ta ja jiki tana duban Hajiya Layla har ta isa dakinta. Mikewa Hajiya Layla tayi tana kai kawo cikin falon hannayenta take hadawa waje daya tana bugawa wani irin yanayi take ji a jikinta sosai taji dadin maganar nan da Areefa ta fadi mata komai take hangowa ya canza sosai take hango nasara a tsakanin ta da Dr.Erena za ta nuna masa ita wacece kuma za ta nuna masa mace ma daraja gareta a duniyar nan ba kamar yarda ya dauka ba... *_KAMALA MINNA_*😍😍😍 UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA TALATIN. 💕💕 *_Kibiyar Ajali Taken Sone, Ya Mamayen da Gangawa, Yai Min Barin Makauniya_* 💕💕 -- *Hamisu Breaker* Tunda ta dago labulan dakin ta sanyo kai take dubanta da kallo kamar wacce taga bakuwar fuska, sosai ta lura da Mariya cikin yan kwanakin nan gabadaya ta sauya kamar ba ita ba sai sanyi jiki da rashin son magana ko aiki take yi haka take zama wata sukuku duk ta rame sai idanu da sukayi mata zuru-zuru ga tsayi da takuma yi sosai. Gyaɗa kai Umma tayi kafun ta kau da kanta daga kallon da takeyi mata sosai ta fahimta sosai ta gane akwai abin da ke dawainiya da 'yarta wanda yake haifar mata da damuwa sosai a zuciya da ma jiki baki daya ba ta san mai Mariya take nufi da hakan ba ba ta san wacce irin rayuwa ta daukarwa kanta ba na zama cikin damuwa sosai ita kanta abin ke damunta a zuciyarta sai dai tana boyewa ne saboda ita Mariyar domin ba ta bukatar ta ganta itama cikin damuwa abubuwa da yawa suke nukurkusar zuciyarta musamman batun mahaifin Mariya ba shi babu dalilin sa anyi cigiyar amma ina ta sha fita ba tare da kowa ya sani ba ta nufi cikin gari amma ina haka take dawowa jiki a sage tasha zama tayi kukan dare domin rage radadin dake damunta in abun yayi mata yawa alwala take daurowa ta kaiwa Allah kukan ta akan ya bayyanar mata da mijinta in har yana raye a filin duniyar nan. Wasu kwalle taji sun kawo mata ziyara cikin idanuwanta da sauri ta shafe su kafun Mariya ta gani. Dago kanta tayi tana duban Mariya dake tsaye tana zare hijabin makarantar da ta dawo kafun ta zube kan katifar tsakar dakin idanuwanta gabadaya ta daga sama tana kallon rufin dakin. "Mariya!". Umma ta fadi cikin wata irin murya mai zurfin gaske tana sauke idanuwanta akan Mariya da ta dago tana dubanta daga kwance. "Tashi mana magana nake so muyi". Wani irin yatsine fuska tayi kamar wacce zata fashe da kuka gabadaya bata so taji ana yi mata magana komai take ji ba dadi zuciyarta take ji wani iri tana yi mata ciwo mai girman gaske bata so a fiye tuhumanta akan abin da ke damun ta domin bata da abin da za ta iya cewa tasan Umma kuma tambayar ta za tayi gabadaya sai taji wani ba dadi a hankali ta shiga kokarin tashi tana cizon laɓɓanta kamar zata tsinke su zama tayi sosai kanta a kasa domin bata bukatar Umma ta gane yanayi da take ciki domin ta tabbata duk wanda ya kalli idanuwanta sai yayi zargin wani abu daban ita kanta ta san tana cikin tashin hankali sosai take jin canji yanayi a jikinta sosai ta lura da komai nata ya sauya ji take yi kamar ba ita ce ba zuciyarta take ji tana wani irin ciwo mai matukar raɗaɗi da zafi ga kasar ruhinta da yake furzar da wani zazzafan huci. "Mariya akwai abin da kike boye wa a ranki, wanda kika kasa bayyanar dashi a filin rayuwarki na lura dake kusan wata guda kenan gabadaya kin sauya kamar wacce bata da lafiya Me yasa haka?". Umma ta fadi cikin sanyin murya Mariya kamar jira take yi Umma ta idar sai hawaye shar-shar sun fara zubo mata wani kuka take ji yana zuwa mata da sauri ta kai hannunta tana rufe bakin nata zuciyarta taji tana yi mata wani irin zafi da raɗaɗi kamar zata fasa kirjinta tayo waje kanta taji yana juya mata komai take kin na filin duniyar yana zama kunci a gareta ji take yi kamar ta mutu ta huta da wannan rayuwar ta duniyar nan ita kanta ta sani tana cikin tashin hankali zuciyarta ciwo take yi ciwo mai girman gaske wanda ko tantama ba tayi shine ajalinta. Ware idanu Umma tayi sosai tana kallon ikon Allah wai na kwance ya fadi hawayen da take gani a fuskar 'yarta ya sanyata faduwar gaba. "Yaa Salam! Mariya meye haka nake shirin gani hawaye a idanuwanki da girman ki me aka yi miki har haka ya sanya ki zubda hawaye". Runtse idanu tayi tana jin yarda zuciyarta ke zafi da wani irin huci kirjinta take ji yana kartawa da wani tashin hankali mai girman gaske. Laɓɓanta ta shiga motsawa sosai muryarta tayi rauni jikinta har rawa yake yi. "Inda mahaifina na filin duniyar nan ba yarda za ayi na kasance a haka, inda mahaifina na kusa dani ba yarda za ayi rayuwata ta kasance a haka, inda mahaifina na filin rayuwata ba wanda ya isa ya saka ni gaba ya dasa min ciwon rai. Ban san me ke kokarin shigowa rayuwa ta ba, Ban san me yake shirin faruwa dani ba, ban san wani irin BALA'I bane yake zawarcin rayuwa ta ba...". A firgice Umma take dubanta kamar wacce ta ga sabuwar halitta wani irin bugu take jin zuciyarta nayi daga kirjinta sosai taji duniyar na juya mata tsoro take ji yana kara girma a gareta komai taji lokaci guda na duniyar na juya mata tsoronta daya ba damuwar batar Mijinta bane ya sanya 'yarta cikin tashin hankali har haka gabanta taji ya sauya bugu da sauri-sauri a hankali ta shiga nuna Mariya da hannu idanuwanta na kawo kwalla ita kuwa Mariya sai kaar sautin kukan ta take yi kamar wacce ake bugu. "Mariya karki ce dani damuwar rashin mahaifinki ce ta kai ki har haka, karki ce dani jarabawar da Allah ya dorawa rayuwarki kike kokarin butulce masa karki ce mani kin kasa YARDA DA ƘADDARA ba fa ke kadai wannan abun ke damu ba ni fa Mijina ne shi kadai ne yayi mani saura a rayuwata bani da kowa sai shi akan sa na rasa iyaye na ga shi yanzu shima na rasa shi amma nayi TAWAKKALI na mikawa Allah kuka na domin shi kadai ne zai yi mani duk wata maganin matsalata Mariya ki sassautawa rayuwarki rayuwa bata son a dauke ta da zafi ke fa yarinya ce wacce take matakin kuruciyarta. Bai kamata ace kin matsawa rayuwa ba karatu kike yi ya kamata ace kin ajje komai a gefe ki bar komai a zuciyarki sannan ki mikawa Allah lamarinki". Sosai Muryar Umma tayi sanyi zuciyarta take ji tana zafi da wani irin raɗaɗi mai girman gaske mikewa tayi kan kafafuwanta tana jin yarda idanuwanta suke kawo ruwa ficewa tayi daga cikin dakin domin ba za ta iya zama ba ta tabbata in ta zauna dukkannin su sai an rasa mai rarrashin dan'uwansa a cikinsu. Kwanciya Mariya ta koma tayi tana faman ajjiyar zuciya mai sanya kirjinta zafi sosai runtse idanuwa ta tayi ba abin da take hangowa sai tashin hankali mai girman gaske a bangarori UKU wanda suke shirin haifa mata da BALA'I UKU. Ba ta san ya rayuwarta zata kasance ba cikin lokacin nan ba ta san ya za tayi ba sosai komai ya tsaya cak! a kwanyarta ina ma ta san a shafin rayuwarta akwai wannan masifar da ta roki Allah ya kasheta tun a cikin Ummanta ba ta san haka duniyar take ba da kwazazzaban tashin hankali da bata shigo ta ba amma ina ikon Allah sai kallo duk mai sauran rai a duniyar nan yana DA SAURAN KALLO. Iskar da taji ta shigo cikin dakin ne ya sanyata sauri buɗe idanuwanta da suke rufe sun kaɗa sunyi jajir kofa ta kalla Hafsi ta gani tsaye tana watsa mata wani irin kallo tana faman yatsine fuska gami da tsaki sosai ta hango kiyayya tsantsa cikin idanuwan Hafsi tun da take da ita bata taba ganin tayi mata irin wannan kallon ba mai cike da tsana da sauri ta tashi zaune tana cizon laɓɓa. "Yo me akai da maza, ai yanzu a ka fara zaman kishi da uwar miji, ki je waje ana kiran ki". Tana fadin haka ta buga wani uban tsaki kamar zata tsinke harshen ta ta fice daga cikin dakin. Fakare Mariya tayi tana kallon ikon Allah wai uwar miji da cin kazar amarci wasu hawaye taji sun zuba mata a zuciyarta ta na ayyanawa anya tana da sa'a a filin duniyar nan anya kuwa ba wani laifi tayi wa ubangiji ba yake hukuntata ta wannan hanyar. "Astagafurullah wa'atubu ilai". Ta shiga fadi kafun ta shiga kokarin komawa ta kwanta tayi luf! kamar wacce bata numfashi tunanuka ne taji sun addabi zuciyarta da kwanyarta da sauri ta mike tana goge fuskarta ta zura hijabin ta akan kayan makarantar da ba ta cire ba waje ta fito ta zira takalmin ta tana dube dube kafun ta jiyo karar saukar ruwa cikin bandakin su ajiyar zuciya ta sauke don ta tabbata Umma ce a hankali tayi hanyar waje Hafsi dake tokare bakin kofa tana kallonta wani mugun tsaki taja fuskarta a hargitse kamar zata fashe da kuka ta juya ta koma cikin dakin kamar wata sabon kamu bakin gadon karfe ta zauna ta na faman turo baki gaba tana wani kumbure-kumbure kamar zata fashe. Dubanta Goggo Marka ta shiga yi da mamaki ganin yarda take hauhawa kamar fulawa taji yis. "Ke kuma meye haka na ga sai faman hawa kike kamar fulawa?". Sake turo baki tayi gaba tana buga kafa a kasa. "Haba Goggo wai ni nafi kowa bakin jini ne a garin nan ace kullum nikenan ina zaune ko matayi babu". Zaro ido Goggo Marka tayi tana ajje kaɗin da take yi kafun tashiga sallallami tana tafawa hannaye baki sake. "Muhammadu dan abdullahi me nake shirin gani Hafsi". Kau da kai tayi tana turo baki gaba. "Ni gaskiya na ga ji kina kallon Mariya sai zarya samari masu zunduma-zudunman motoci suke mata jiniya a kofar gida nikuwa ko 'ya'yan gidan Malam Shehu bana gani". "Iyee to ai shikenan bara na zo na sanya a rubuce miki suratul-Yusufa ki shanye tun da kin rasa mashinshi ne sai mu ga yarda Allah zai yi". Goggo Marka ta fadi tana mai bankamata harara kamar idanuwanta za su zubo kasa. "nifa gaskiya Goggo kisan yarda za kiyi dani ba yarda za ayi ace Mariya ta fini farin jini samari kanta kawai suke zarya nikuwa kamar na hadiyi jaɓa don bakin jini dame ta fini ki duba fa ki gani". Ta fadi tana mai mikewa tana jujjuya jikinta. Mamaki fal! zuciyar Goggo Marka gabadaya ta rasa ma abin da zata ce sai faman bin Hafsi take yi da ido ba tayi zaton Hafsi za tayi haka ba ba taba zaton irin wannan maganar zata fito daga bakinta ba ba kunya ba tsoron Allah. Girgiza kai tayi tana mai sake duban Hafsi kwalla ta gani a idanunta tana yatsine fuska kamar zata rushe da kuka da sauri ta ware idanu ciki da tu'ajibi. "Samarin Mariya Uku kuma duk masu Mota ni kuwa ko mai keke bani dashi ni gaskiya ba zan yarda ba ni dai kawai ki san yarda zakiyi dani na gaji nima saurayi nake so na ganni dashi in ba haka ba ai sai Mariya ta rainani sosai da sosai". "Ya isa haka Hafsi yi shiru zauna muyi magana". Turo baki tayi tana zauna sai faman kumburi take yi. "Ke kina da wanda kike so?". "Na fa ce miki ba wanda yace yana sona sai fa kwanaki Danliti mai gini yace wai ni yake so ni kuma ba abin da zan yi dashi katon hanci gareshi ga kunnuwa fala-fala". Kuri Goggo Marka tayi mata dariya ta so kama ta amma sai ta kanne tana mai cewa. "Naji to ke yanzu wa kike so?". farrr! tayi da idanunta tana mai saka dan yatsa cikin baki kamar mai son tunano wani abu kafun ta dubi Goggo. "ni so nake yi na samu mai mota irin na Mariya ko ma ta ban saurayin ta guda daya a ciki". "Shikenan waye a cikin su kike so nayi miki Alkawari zaki same shi Hafsi farin cikinki shine nawa yo me akayi da waccan mai kalar zazzafin shawarar ki sha kurumin ki ko duka samarin kike so zaki mallake su....". Wani ihu tayi tana mai kaiwa Goggo cafka tana rungume ta sai faman kyalkyalar dariya take yi. "zo muje na zabi wanda ya zo yanzu gashi can a waje zo muje ki ganshi mai kyau ne motarsa luntsumemiya gashi dan gayu". "Nifa tsiyata dake gajen hakuri wallahi Hafsi me zamu je yi kuma ke dai kwantar da hankalin ki kamar kin yi bako ya mutu ki bar komai a waje na shi da kansa zai zo yana rokonki ki so shi". Wata irin dariya ta sake yi kafun ta mike tana tikar rawa. Ita dai Goggo Marka baki ta saki tana kallon ikon Allah. Tsagaitawa tayi da rawar da take yi ta shiga dube-dube kafun ta hango abin da take so kwanon soson wanka ta dauka tana duban Goggo Marka sannan ta fice. Goggo Marka ta margaya kai tana mai fadin. "ai sha kuruminki magana ai kuma ta kare mata tace da mijinta shege". ****** Tun da Mariya ta doshi soron gidan su take ji gabanta na tsananta faduwa sosai take jin wani iri kamar ta koma amma wani sashi na zuciyarta na ingizata da taje ta gano waye sai da ta tsaya ta numfasa gami da saita kanta sanan tayi shahadar kuɗa ta fice gabadaya fuskarta a kasa. Tsaye yake jikin motarsa kansa na duban takalman dake kafarsa kallo daya zakayi masa ka gano irin ramar da yayi sosai da sosai ya kara haske duk da duhun fatar da yake da ita takun da yaji ne ya sanya shi dago kansa a daidai lokacin ita ma Mariya ta dago kanta gabadaya suka sarke juna da kallo zuciyoyinsu suka shiga bugu da sauri-sauri kowa ya kasa dauke ido daga kallon dan uwansa sai da suka shafe tsayin lokaci kafun Mariya taja wani dogon numfashi kafafuwanta taji sun shiga rawa sosai ji take yi kamar zata zube kasa. "Yaa Rabbi!". Ta furta cikin wani irin yanayi na rashin hayyaci a hankali tashiga juyawa domin komawa cikin gida gaban ta ji yana duka ba ta san abin da yasa ta fito ba, bata san ya akayi ba ta fito ba ba tare da ta san waye ba tajima da ajje Huzaif a gefe duk da kullum zuciyarta sai ta yi mata tunanin shi bata so ace sun sake haduwa ba domin bata bukatar sake ganinsa domin ganin sa ba karamin sanya ta yake yi cikin tashin hankali ba. Ciwon zuciyarta daɗuwa yake yi tashin hankalin ta karuwa yake yi duniyarta sake rikicewa take yi a duk lokacin da tayi arba da Huzaif ba ma Huzaif ba duk wani wanda yake da takomashin sanya zuciyarta tashin hankali. "karki yi mani haka Mariya zuciyata zata iya bugawa a ko wani lokaci in har kika ki tsayawa ki saurare ni ban san ya ba zuciya tana kuna ruhina na ciwo gangar jikina ya zama kamar ba nawa ba". Numfasa yasake yi yana jin yarda kirjinsa ke harbawa da duk wani tashin hankali da yake ciki zuciyarsa ciwo take masa ciwo mai tsanani. "Rayuwata na cikin hatsari komai nawa ya shiga ruɗani ban san ya zan kwatanta miki tashin hankalin da duniya ta take ciki ba na rokeki ki saurare ni Mariya". A hankali ta fara tsaigatawa da tafiyar da take yi gabadaya taji duniyar na juya mata kafafuwan take ji kamar suna narkewa jikinta rawa yake yi zuciyarta lokaci guda ta sauya da bugu tana buɗe shafin da ta baiwa Huzaif ya zauna a ciki runtse idanu tayi tana jin yarda zuciyar ta ta ke kartawa kamar ana soka mata KIBIYAR AJALINTA. A hankali ya shiga takowa yana jin yarda bugun zuciyarsa ke canza bugu da wani irin yanayi game da Mariya numfashi yake ajjewa da duk kamshi da yake ji yana tasowa daga jikin Mariya yana haifar masa da wani irin yanayi na kasala a jikin sa da zuciyarsa gabanta ya karaso ya tsaya yana mai juya idanuwansa da suka kaɗa kadan fuskarsa cike da yanayi na rauni hannunsa ya kai saitin in da yake zaton zuciya na wajan ajje. "Mariya kin ga nan dina ji nake yi kamar KIBIYAR AJALI ake sokamin ji nake yi kamar KASKON WUTA ake sauke mani a wajan Mariya sosai nake jin wani iri a game dake sosai nake jin zuciya tana kara buɗe fili mai girman gaske a game dake komai ma da komai na zuciyar ke ce a cikinsa...". "Ya isa haka Huzaif ya isa nace maka na gaji da jin wannan kalaman ka bar ni haka in har ba so kake yi kwanyarta ta tarwatse ba in har ba so kake yi zuciyata ta buga ba na mutu hankalin ka ya kwanta". Numfashi ta shiga ja ta kai hannayenta duk biyu tana rufe bakinta jin kalaman nasa take yi kamar saukar narkakkiyar dalma a zuciyarta jin sa take yi kamar yana doka mata ganga mai matukar kara a cikin kunnuwanta sosai taji bugun zuciyarta ya sauya komai take ji na jikinta yana narkewa kamar ruwa. 'Yaa Allah'. Ta furta a can kasar zuciyarta da take ji tana kecewa da tashin hankali mai girman gaske. "Mariya...". "Nace maka ya isa haka ka bar zuciyata ta huta mana Huzaif". Ta sake katse shi tana toshe kunnuwanta da take ji kamar za su tsinke. Runtse idanu Huzaif yayi yana jin sautin muryarta na amsa sauti mai girma a kunnuwansa da kwanyarsa sosai ya ji zuciyarsa na bugawa da yanayin da Mariya take nuna wa a gareshi numfashinsa yake ji ya canza yanayi yana sama da kasa kamar zai dauke cikin yanayi na ciwo yake cizon laɓɓansa. "Baki so na ko Mariya baki kauna ta bakya son gani na a filin duniyarki ko kiyi hakuri zuciyata ce ta matsa min zuciya ta kasa hakuri gabadaya ta hauka ce a dalilin ki ba ta jin sautin komai sai naki Mariya ki taimaka Huzaif din ki ne fa". Ya karashe muryarsa na karyewa da yanayi na son kuka a hankali yake hadiyar wani abu mai tauri da ya tsaya masa a kirji zafi yake ji zafi na sosai da sosai kansa yake ji yana kokarin darewa biyu nauyi yake ji yayi masa ji yake yi kamar bana sa ba. A hankali ya fara juya yana kai kawo kamar wani sabon hauka. "Ban sani ba ashe zuciya ta tayi ganganci, ban san zuciya ta hauka take yi ba, ban san wai dama hauka nake yi ba, ban san dama ban dace da wajan da zuciya ta kawo ni ba, ban dan dama ni kadai nake jin irin wannan yanayin ba a zuciya komai nawa ya sauya ya canza kamar bani ba, kamar ba Huzaif ba duniyar ta yi wani iri ba dadi komai ma ba dadi". Sosai Mariya ta tsorata da yanayin da taji yana sambatu idanuwanta sosai suka fito waje kanta ta ji ya shiga juyawa kamar zata zube kasa runtse idanu tayi zuciyarta na wani irin bugu da sauri-sauri. "Yaa hayyu Yaa Kayyum". Kawai take fadi wasu zafafan HAWAYEN ZUCIYA ne taji suna saukar mata jin su take yi kamar tafasassu. "Shikenan Mariya na tafi...na tafi tun da ba ki son ganina na takura miki ko yi hakuri shikenan na tafi". Ya fadi yana mai daga mata hannu murmushi a fuskarsa mai sanya zuciya ciwo mai girma a hankali ta shiga motsa laɓɓanta. "Huzaif!". Ta fadi da wani irin yanayi mai girman gaske cak! Ya tsaya yana mai juyowa gabadaya idanuwansa sun kaɗa sun yi jajir. "Kar ka tafi kayi hakuri karka ga laifi na nima ba yi na bane laifin zuciya tane ban san ya zan yi ba komai ya kulle a cikinta ta kasa daukar komai ma". Duban ta yake yi da wani irin yanayi cikin idanuwanta yake hango wasu abubuwa masu girman gaske su na sanya jikinsa narkewa da wani irin yanayi. Baki ya shiga motsawa yana nuna ta da hannu magana yake son yi amma ya kasa sai faman girgiza kai kawai yake yana sakin wani yaƙe mai girma a fuskarsa. Wani dogon tsaki suka ji an saki duk kan su suka juya suna duban in da suka ji sautin na tashi. Hafsi ce tsaye ta rike kugu sai faman kumburi take yi kamar zata tarwatse wani kallon tsana da ƙi ta sake jifan Mariya dashi tana faman huci kamar kububuwa kafin ta juyar da kallonta wajan Huzaif tana kare masa kallo zuciyarta take ji tana shiga yanayi game dashi girgiza kai tayi tana mai tsartar da yawu a hankali ta juya tana kallon Mariya ita ma ita take kallo cike da mamaki da tu'ajibi. "Huzaif sai anjima" Mariya ta fadi cike da wani yanyi mai ciwo yana kokarin yin magana amma ina har ta shige cikin soro duban Hafsi yayi cikin haushi da takaici ji yake yi kamar ya shake ta don bakin ciki dunkule hannu yayi yana bugun iska yana mai cizon laɓɓa da sauri ya juya jikin sa sai kyarma yake yi ya isa wajan motarsa a hanzarce yayi mata key ya fizge ta rai bace har yana baɗe Hafsi da kura ya bar unguwar. Wata irin shewa tayi tana tafa hannunta sannan ta juya cikin sauri ta fada cikin gida ranta fes!!... *_KAMALA MINNA_*😍😍😍 [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA TALATIN DA DAYA. Tsaye tayi ki kam!. tana faman yatsine fuskarta da cizon laɓɓanta sai faman ajiyar numfashi take kamar wacce tayi Gudun ceto rai. "Ni wallahi gabadaya na gaji". Ta fadi tana mai jingina da bishiyar dogon yaron dake bakin hanyar da zata fiddo su daga cikin surkuk'in dajin da suke. kallo daya za kayi wa wajan ka tsoro ta sosai musamman in ka kasance mai karyayyiyar zuciya in aka ce ka shigo wajan ko da kudi ne ba zaka shigo ba daji ne sosai mai dauke da surkuk'in ciyayi da dogayen bishiyu kamar su sukayi kansu ga wasu gingima-gingiman duwatsu suma abin dai na tsoro gashi nan ba kajin kukan komai sai na gyare da tsintsaye. Tsaya tayi da tafiyar da take yi jin abin da Hafsi ta fadi ta juyo kallo daya zakayi mata ka gane itama ba karamin gajiya tayi ba sai faman numfarfashi take yi jin jikinta take kamar wacce akayi wa dukan kawo wuka. "Ke kam kin fiye tsirfa wallahi ni ban ce na gaji ba sai ke mai jikin kuruciya kai jama'a ke dai kam anyi ranguwa wallahi Hafsi". Sake turo baki tayi gaba tana kokarin zama gindin bishiyar. "Haba mana Goggo Marka ki dubi uwar tafiyar da muka dauko fa aiko akan abun hawa muke wallahi sai mun gaji ga kuma fargaba da tsoro ki dubi dajin nan fa ki gani ba kowa bane zai iya shigarsa ko ni dai na shiga a tsakanin rayuwa ko mutuwa wallahi ban ma yi tunanin zan fito ba don tuni na fara dankaro salati a bakina...". Cak! ta tsaya da maganar da take hango maciji tayi saman jikin bishiyar da take jingine wata irin razananniyar kara ta saki idanuwa warware Goggo Marka dake rike da kugu jin ihun Hafsi ya sanya Goggo Marka shekawa da gudu tana tsalle tsalle kamar wacce abu ke biwa kafa dama tuni a tsorace take tun da suka shigo cikin dajin gabanta ke faman dukan luguɗe. Ihun Da Hafsi ta cigaba da yi ne ya sanyata tsayawa can gefe tana faman numfarfashi tana bin ko ina da kallo. "Ke Hafsi Lafiya kike kuwa". "Maci...ji neee". Ta fadi cikin rawar baki da na jiki da sauri Goggo Marka ta sake fallewa can gefe tana mai cewa. "Rugo ki baro wajan mana tun kafin ya illata ki in ma zaki iya kashe shi kawai...". Ai ba ta karasa abin da take cewa ba itama kurma ihu jin abu ya taba mata kafa. "Laha'ilaha 'ilallahu muhammadan rasulullahi Sallallahu alaihin wasallam". Kam! ta kame a tsaye lokaci guda fitsari ya fara bin kafafuwanta. Hafsi dake can gefe tana faman kurma ihu da tsalle-tsalle kamar wata biri lokaci guda ta fallo a guje tana mai wurgi da kallabin dake kanta zaninta kuwa gabadaya ta tattareshi ta cukuikuye zuwa kugunta a haka har ta iso wajan da Goggo Marka take a kame kanta tayi tana rungume gabadaya ta ma k'yalk'aleta ji kake rigija sun zube a kasa hakan ya dawo da Goggo Marka hayyacinta ta shiga ihu tana mai cewa. "Ya sare mani kafa shi kenan na bani na lalace shikenan Alkiyamata ta zo wayyo ni kai na...". Hafsi ta gani zube gefe guda tana faman sakin numfashi gami da dariya ya sanyata yin fakare da idanuwa jikinta sai k'yarma yake yi a hankali ta shiga jan numfashi tana mikewa kafun ta gyara daurin zaninta. "Ba dai ya sare ki ba ko Hafsi". Ta fadi tana bin sassan jikinta da kallo Hafsi ce ta sake kecewa da dariya tana mikewa har lokacin jikin nata bai daina bari ba. "Goggo menene haka a jikin ki?". Jin abin da Hafsi ta fadi tana zare ido ya sanya Goggo Marka sakin sallallami tana tsalle kamar wata biri hakan ya kara baiwa Hafsi dariya har tana rike ciki ganin hakan ya sanya Goggo Marka dubanta tare da yi mata dakuwa don ta lura kawai so take yi ta firgita ta. "Fitsari fa Goggo Marka". Ta sake fadi tana kwashewa da Dariya sai a lokacin ta lura. "Ikon Allah". Ta fadi tana mai juya zanin nata da yayi jagaf!. "kai Goggo Haka kike da tsoro ashe har na fiki dauriya ma". Harara ta galla mata. "ke dalla jaye wahala ba dadi gareta ba, kuma ai tsoro halas ne wallahi ke yanzu in macijin nan ya gaftaramin sara ai sai dai buzu na... Kin ga tashi mu bar wannan azababben dajin tun kafin almatsutsan cikinsa su saukar mana akanmu mu bani mu lalace". Ta fadi tana mai tattare zaninta da yayi jagaf! Takalmanta a hannu a hankali take taka kasa tana mai dube dube. Tafiya sosai sukayi kafun su fito hanyar da za ta kai su bakin titi nan ma sai da suka zauna suka huta sosai Hafsi sai faman kwakwazo take yi akan ita fa ta gaji bayan ta kamar zai karye haka take ji duban ragwanta Goggo Marka tayi mata. "Ke dai akwai sakankiya wallahi na dauka duk ke ake yi wa wannan wahalar amma kin ishi mutane da ihu kin gaji". Turo baki tayi gaba tana kau da kai a hankali ta mike daga zaman yan borin da tayi ganin Goggo Marka ta dauki hanya ko magana batayi mata ba. Sun yi tafiya mai dan tsayi kafin su isa bakin titi nan Goggo Marka ta shiga neman tsayar da Mai tasi domin shiga kowa ta tsayar ta sanar da shi inda zata sai ya ce a,a tun tana tsaye har taji ta fara gajiya amma ba su samu mai tasi ba ita kuwa Hafsi na can gefe yashe sai faman numfarfashi take yi. "Don Allah taimaka". Ta fadi lokacin da wani mai Tasi yayi slow daidai su jiki na bari ta isa gareshi. "Gwada zaka kai mu don Allah". Dubanta yayi sosai kafun ya dubi Hafsi. "Iyaka ta Kauyen Mutum Daya ba zan shiga Gwada ba". Ware idanu tayi tana mai yin kasa da murya. "Haba d'ana taimaka don Allah wallahi mun jima a nan zaune ba mu samu abin hawa ba duk mun gaji ga rana ka ga jikanyata can ma zaune tana numfarfashi". Dubanta yake yi sosai yana sake duban Hafsi a hankali. "Nawa za ku bayar?". "Naira dari za mu baka". Tsuke fuska yayi lokaci guda. "nifa ba zan shiga Gwada ba sai dai in sauke ku a Mutum daya ku nemi wata motar ta karasa da ku". kara kashe murya tayi tana kokarin masa magiya yayi saurin tare. "Allah ba zan je ba in zaku shiga na kai ku mutum daya to in ba kwaso nayi gaba". Shiru tayi tana tunani kafun ta juya ta dubi Hafsi da ta zuba musu ido tana jin komai gyada kai tayi alamun su je kawai da babu gwara ba dadi kuma a saka a baka yafi a rataya. Haka suka dunguma cikin motar Goggo Marka sai faman tsaki take yi tana gunguni wai dan tasi din ba shi da tausayi tana tsohuwa amma ba zai taimaka mata ba gashi ya tsula musu kudi. Ba wanda ya kulata haka ta karaci maganar ta tayi shiru a haka har suka isa Mutum daya suka sauka ba su fi mintina biyu ba suka samu motar Gwada nan ma sai da aka kai ruwa rana da direba don ya lura Goggo Marka yan son banza ce shi kuwa ya nuna mata ya fi ta son kudi ko bakano haka ya ganshi ya barshi. Haka tashiga motar tana ta mita shima sai masifa yake yi mata yana hadawa da yarensa na yarbanci abu yaki ci yaki cinyewa kamar cin kwan makauniya ganin da yayi ta zage sai surfa ruwan bala'i take ana bata hakuri amma ina aiko ya ja burki yace ta fice masa daga mota. "kai kam anyi watsantsan d'a wallahi dan bakin mugun abu". Ta fadi a zuciya amma a fili sai tayi lakwas ganin haka ya sanya sauran fasinjan baiwa direban hakuri haka ya koma ya ja motar yana faman jan tsaki kamar harshensa zai katse. ******** *9/MAY* *_WATA ALKARYA_* Tunda ga ne sa zaka hango tsilli tsille na tamfol da aka kankafa kamar dakuna wani saman tamfol kuma a kwai tuta dake kafe akai an rubutu sunan Malik bin yazid da rubutun arabic sosai wajan yayi tsit kamar ba kowa sai mashina kiran bajat dake warwatse a tsakar wajan ko wani tamfol daya kuwa an kewayeshi da ginin dutse wanda ya kusan rufe shi can gefe guda kuma wani tamfol din ne amma duk yafi sauran girma da fadi nesa ba kusa ba. Zaune yake jikinsa sanye da bakar jallabiya fuskarsa cike take da kasumba ga wani gemu ajje sosai ya naɗe kansa da farin kyalle mai laushi sosai idanuwansa jajaye ne fuskarsa daure tamau kamar bai taba dariya ba gefensa bindigogi ne kirar Ak47 kusan biyar. Duban mutumin dake durkusa gabansa yayi da wani irin kallo mai razanar da wanda akayi wa shi yana mai fadin. "Baaba BG nayi maka gargaɗi na farko kuma na karshe a wannan alkaryar ban taba samun matsala da duk iyalan kungiyar nan ba sai kai a karo na uku kenan ina sanyaka aiki kana bani matsala ban san me kake nufi ba ya kamata ka sani wannan alkaryar da ka shigo ba a sassauci sannan ba a saka mutum aiki ya kiyi rayuwar saida rai ce a wannan sansanin rayuwa ce ko mutuwa ya kamata ka sani jahadi kake yi ko mutuwa kayi a wannan hanyar ka zama shahidi". Ya karashe yana mai dago daya daga cikin bindigun da suke yashe gefensa kafun ya daga zuwa sashi da kuka yake tashi lokaci guda ya saita jikake durum ya dauke mai kukan can gefe guda kansa yayi fata-fata kafafuwansa sai motsawa suke yi kafun su kame lokaci guda. Wani dan kyalle ya dago yana mai goge jikin bindigar kafun ya saki wani murmushi mai zafin gaske yana duban Baaba BG da yake sunkuye jikinsa sanye da jallabiya kansa da rawani fuskarsa cike da kasumba ba ka iya gane asalin fuskarsa saboda tulin suma da ya tara. "Ka sani ba zan yarda da wannan gangancin naka ba domin kuwa a ko wani lokaci zan iya dauke ka daga duniyar nan kamar yarda na dauke waccan yarinyar da take wa mutane ihu". Har zuwa lokacin Baaba BG bai dube shi ba kan sa na kasa sai faman jan numfashi yake yi. Motoci ne kirar Sharon suka shigo wajan a jere guda uku ko wacce da tuta a jikin ta can gefe guda sukayi parking kafun su fara fitowa da ɗaiɗai ko wanne cikin su fuskarsa yane ba ka iya gane su hannayensu dauke da manya manyan bindigogi daya daga cikin su ne ya fara takowa har ya iso in da shugaban nasu yake ya zube a kasa kamar zai masu sujjada. "Yah Shugaba mun kammala komai". Gyaɗa kai yayi kafun ya daga kai yana kallon yarda ake fiddo da mata matasa daga cikin motocin jikin su sanye da kaya iri daya kallo daya zakayi musu ka gane yan makaranta ne wacce fuskarta cike da tsoro wasu ma sai rusar kuka suke yi. Murmushin gefen kunci yayi kafun ya mike kan kafafuwansa ya fara takawa kamar wani mai ji da sarauta da mulki har ya isa wajan izuwa lokacin an gama fiddo da su akalla za su kai dari da yan kai jera su akayi ya shiga bin su da kallo daya bayan daya yana kara fadada murmushin fuskarsa. "Kun tabbata dukkansu ku ka kwaso". Duban juna sukayi su duka kafun su gyada kai alamun 'eh' daya daga cikin su ne ya dora da cewa. "Yah Shugaba yanzu haka ma kauyen Sarwadi mun tayar dashi ba wani wanda yayi rai a cikin su. Murmushinsa ne ya sake faɗaɗa kafun ya sanya hannu ya fizgo daya daga cikin matar wacce ta kasance ita kadai ce mace mara hijabi da cikakkiyar suttura sosai ya damki gashin kanta yana ja kafun ya yi wani gurgi da ita ta baje a kasa gami da sakin wata razananniyar kara mai sauti gaɓadayan sauran suka shiga ihu su ma suna kokarin tarwatsewa da sauri fizgo bindiga daga hannun yaran nasa ya shiga sakar musu wuta ciki zafin nama kawai zubewa suke yi a kasa kafin wani lokacin duk rabin su ya bajar da su akasa sauran kuwa takurewa sukayi waje daya wasu ba su daina gudu ba suka yanki cikin dajin sosai suna faman ihu da kururuwa. Wata dariya ya saki kafun ya dubi Sauran Yaran sa. "Kar ku sake daya daga cikin wadancan da suka yanki daji su sake numfashi a doron kasar nan ina son kafin mintina naga gawar su". Kafun ya dire kalamansa wasu su falle da gudu sun yanki daji sauran da ba su tafi ba ya dube su. "ku kwashe dukkan su ku zuba masu sark'a". Yana fadin haka ya juya ya dubi wacca ya damkar wa gashi dazu sai faman rusa kuka take yi jikinta na kyarma idanuwanta sun kaɗa sun yi jajir gefen kanta na zubda jini in da ta bugu sosai. Isa yayi gareta ya dan rankwafa yana mai sakin murmushi kafun wani lokaci fuskar canza ta koma wata kala daban ta tsananin rashin Imani da tausayi kanta ya sake kai hannu ya cafka yana mikar da ita kan kafafuwanta wani ihu ta saki gami da rushewa da kuka wani zafi ne da raɗaɗi da zugi take jin duk wani kafa ta sumar guda daya na fita komai take ji na jikinta yana canzawa kamar bana ta ba ji take yi kamar ba a duniya take ba kamar wata duniya ce ta azaba take ji ita kadai ne a ciki. Haka ya ja ta akasa tana ihu tana komai har ya isa daidai mazauninsa har lokacin Baaba BG na durkushe in da ya barshi cilli yayi da ita waje guda kafin ya dago bindiga ya saita goshin sa. "In har kika sake naji wani abu mai kama da kuka sai na tarwatsa miki kan ki yanzun nan". Ya fadi yana tamke fuskarsa cikin wani irin yanayi na rashin tausayi da imani. Dago idanuwanta tayi da take jin su kamar bana ta ba sun kaɗa sun yi jajir jijiyoyin kanta duk sun fito sunyi raɗa-raɗa abin ka da farin mutum gabadaƴa jikinta ya rine yayi jajir waje guda ta haɗe jikinta ta dunkule zuciyarta na kara dokawa da tashin hankali mai girman gaske ba abin da take tunawa sai yarda aka ci zarafin su aka keta musu mutunci a gaban idanuwansu aka yanka iyayen su a gaban idanuwansu aka bambaka musu kauyensu garinsu da suke zaune cikin kwanciyar hankali lokaci guda an canza musu rayuwa an kaskantar da su an mai da su ko dabbobi sun fi daraja da kima ba ta san yarda zata ce ba bata san ya zata kira wadannan mutanan ba sosai take hango salon da suka shigo masu gari da shi na tsayin sati biyu suna nuna musu suna Allah ne hanyar tsira da dacewa suke nuna musu ashe ba haka bane sai da suka saki jiki da su lokacin guda suka fiddo musu da kudirin su da manufarsu. Wani kuka ne taji ya kufce mata lokaci guda da sauri ta kai hannunta ta toshe bakin ta amma duk da hakan sai da kukan nata ya fito waje runtse idanuwanta tayi cikin sadakarwa jira kawai take taji alburushi ya ratsa tsakanin kwanyarta sosai ta hango yarda a gabanta aka dannewa mahaifinta kirji aka soka masa wuka a makoshi tana kallon yarda suka mai dashi kamar wani kare suka dinga ball da gawarsa har sai da suka ga numfashin sa ya daima motsi kafun su rabu dashi bayan sun cinna masa wuta. Wasu zafafan hawaye take ji suna sauka a kuncin ta lokaci guda kuma taji ana dauke mata su a hankali ta fara buɗe idanuwanta da take jin kamar za su zazzzago kasa saboda raɗaɗi da zugi da taji suna yi mata. Wani razananiyar kara ta saki ganin wanda yake gabanta lokaci guda ta dunkule waje daya jikin ta na faman kyarma idanuwanta na kansa tsanarsa take ji tana tsarga ko wani sashi na jinin jikinta sosai take ji a fadin duniyar nan ba wanda ta tsana kamar sa rokon Allah take yi ya daukar mata ranta da wannan BALA'I da take ciki rokon Allah take yi ya rabata da wannan mugun azzalamun da bai san imani da tausayi ba a zuciyarsa. "Dama kin daina kukan nan domin kuwa yanzu rayuwa ce zaki sauya duniyarki zaki canza komai naki zai canza ki sani wannan wata duniya ce zaki fara rayuwa a cikinta tare dani zaki kasance har zuwa lokacin da nayi raayin rabuwa dake". Hannu ya kai yana kokarin shafe fuskarta a karo na biyu da sauri taja da baya gabanta na sake bugawa lokaci guda ta shiga kankame jikinta tana hadewa waje daya. "ki kasance da Malik Bin Yazid a duniyarki sabuwa". Wani irin zaro idanu tayi waje kamar za su fada birkicewa da rkicewa da razana duk suka gauraya lokaci guda a gareta zuciyarta ta ji ta sauya bugu numfashin taji ya fara fizga cikin tashin hankali magunan jinin jikinta take ji suna yin kasa suna tsayawa cak! jikinta take ji yana narkewa kamar ruwa sunan da taji ya ambata ya shiga ansa amo mai sauti a kwanyarta lokaci guda numfashinta ya tsaya cak! ta sankare a wajan. Ta jima cikin wannan yanayin kafun ta ja wani numfashi mai tauri kirjinta taji yayi mata nauyi har zuwa lokacin idanuwanta na kansa shikuwa sai faman murmushi yake yi don ya luta da razanar da tayi. 'Malik Bin Yazid' Ta fadi a zuciyarta sosai ta gane sunan sosai ta tuna sunan. sunan da ko fadin sa akayi dole ka shiga tashin hankali saboda irin tashin hankalin dake tattare dashi ba zata manta wannan sunan ba sosai tajima da haddace shi sosai ta gane shi rikakken dan ta'adda da ake nema RUWA A JALLO mutumin da ya addabi al'umma mutumin da ya kasance masifa da bala'i a rayuwar al'umma ya hana su kwanciyar hankali da natsuwa yana rayuwarsu tafiya yarda ta kamata mutumin da ya haifar da bala'i da rashin kwanciyar hankali ga zuciyoyi masu yawa mutumin da ya haifar da ciwo mai girman gaske a zuciyoyi masu yawa shine Allah ya hada ta dashi ita ce yau tare dashi rayuwar tace ta juye zuwa duniyarsa ita kuwa wata irin mummunar ƙaddara ce ta fado mata rayuwa ita kuwa wani irin BALA'I ya fado mata rayuwa a daidai wannan lokacin bata san mai za ta ce ba bata san ya za ce da wannan ƙaddarar ba ta sani rayuwarta ta kare komai nata ya sauya zuwa tashin hankali da bala'i ta sani tayi bankwana da farin ciki tayi bankwana da kwanciyar hankali ta rabu da iyayenta har abada ga shi yanzu ita kuma ƙaddararta ta jona ta da wannan bala'in wanda ba ta san ya zata kwatantashi ba. Gyada kai ta shiga yi idanuwanta na fiddo da wasu hawaye masu tsananin zafi da kokarin yayyaga mata fatar fuska duban sa take yi da wani irin yanayi mai girman gaske tana ayyanawa a ranta wannan mutumin mai rai daya a jikinsa shine ya addabi miliyoyin mutane ya hana su kwanciyar hankali bata san ya zata kwatatta wannan lamarin ba. "Karki yi tunanin sake wata rayuwa kawai ki saka a ranki kina tare da Malik Bin Yazid". Wani zafi taji kirjinta nayi kafun wani abu mai girman gaske ya zo ya tokare mata kirji dago idanunta tayi tana duban Baaba BG wanda tun da aka kawo su duniyar BALA'In nan ta lura dashi a durkushe har izuwa wannan lokaci tsoho ne sosai wanda wahala da bala'i suka dakusar dashi wajan kara zama tsoho na karfi da yaji fuskarsa kawai ta kalla ta gane bala'in da yake ciki idanuwansa a kasa ko motsin kirki ba yayi wani irin tausayin sa taji ya tsirgar mata da sauri ta kau da kai kafun ta dubi Malik wanda har lokacin yana rankwafe a gabanta. Kallon sosai tayi masa lokaci guda ta ji zuciyarta ta kekeshe da duk wani tashin hankali da take ji komai taji tsaya mata na tsoro kallon sosai da sosai tayi masa kafun ta kau da kai tana jan tsaki can kasar makoshinta. Wani wawan Mari da sanya ta sakin fitsari da ganin taurari taji ya gilma a kuncin ta lokaci guda ta baje a kasa gami da kurma uban ihu. Mikewa yayi zuciyarsa na wani irin tukuki da zafi bindigi ya ciru daga kugunsa karama lokaci guda ya saita ta sosai idanuwansa na bayyanar da wani tashin hankali mai girman gaske runtse idanu tayi tana jiran saukar alburushin domin ta gama sadakarwa ba za ta sake ko da minti daya a duniya nan ba. Tun tana jin tafiyar numfashinta da sauri-sauri gabanta na wani bugu mai girman gaske a hankali ta fara kiran sunan Allah kafun taja numfashi mai girma ta buɗe idanuwanta tsaye ta hangeshi har yanzu bindigar na saitinta amma bai harba ba. Mamaki ya cika mata zuciya sosai ganin yanayin da yake ciki gabadaya idanuwansa na kanta ga bindiga a hannunsa amma ya kasa harbawa kuri tayi masa da idanu tana mai sakin ajiyar zuciya sunayen Allah a laɓɓanta ba ta san ma mai za tayi ba komai take jin yana zama al'ajabi da mamaki a gareta ba ta ankara ba kawai taga ya cafko hannunta ya mikar da ita cikin wani irin yanayi na mazantaka ya shiga jan ta ciki hanzari kamar zai kifata da kasa ita kuwa baki ta saki tana kallon ikon Allah lokaci guda fargaba da razana da tsoro suka shiga tsalle -tsalle a zuciyarta har lokacin da suka iso wajan da Baaba BG yake yashe idanuwa ya dago a cikin galabaitaccen yanayi ya dubeta ita ma shi take duba cikin wani yanayi na tsanani sadakarwa sosai suke kallon juna cikin yanayi na tashin hankali mai girman gaske tana kallon shi yana kallonta har zuwa lokacin da taji Malik ya fizge ta zuwa cikin tamfol din sa yayi cilli da ita a ciki ba komai a cikin tamfol sai hargitse wanda sam ba su dakyan gani bindigogi da alburusai can gefe kuma wata yakunaniyar shimfiɗa ce mai dauke komaitsai da sauri ta dago kai gabanta na cigaba da bugawa tana dubansa shima ina ya ke duba kafun ya ajje kallonsa ga kan shimfiɗarsa. "Zaki kasance dani kamar yarda na sanar dake ki shirya zama dani ki saka a ranki kina tare da Malik Bin Yazid". "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'una". Abin da zuciyarta ta shiga fadi kenan cikin kyarma da tsoro lokaci guda ta shiga matse jikinta waje daya duban sutturar jikinta take yi yarda aka kekketa ta sosai ana hango wasu sashi na jikinta ya bayyana a fili runtse idanu tayi wasu hawaye su ka balle mata. Ta sani shikenan rayuwarta ta kare shikenan duniyarta ta gama k'awa da tashin hankali wnda ba ta san ran fita daga cikin sa A Hankali taji ya fara takowaa kusa da ita gabanta yana tsananta faduwa jikinta sai kyarma yake yi lokaci guda numfashin ta ya fara sama da kasa lokaci guda ta saki razananniyar kara cikin firgici da tashin hankali komai taji ya tsaya mata cak! duniyar tana juya mata bata san abin da ke faruwa ba idanuwanta dai na kansa har lokacin da iso gareta ya rankwafa yana mai kamo hannayenta duk biyu yana mikar da ita a hankali idanuwanta suka shiga rufewa kafun taji jikinta na narkewa lokaci guda tana watsewa a kasa.... 😘😘 *_KAMALA MINNA_*😘😘😘 [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA TALATIN DA UKU Huce mai zafi yake fesarwa kamar wani kumurci. tashi yayi tsaye daga kan kujerar dayake zaune yana bugun Table din dake gabansa idanuwansa sunyi jajir kamar wanda aka yiwa sirace da barkano. "Alhaji Abdulwahaab na fada maka ka fice mani daga cikin Office in kuma ba haka zan yi maka abin da baka taba zato ba". Ya fadi yana mai kara turbuɗe fuskarsa kamar zai cinye shi danye. Murmushi Alhaji Abdulwahaab yake saki mai cike da bakin ciki da takaici wai yau har shine Dr.Erena zai dubi tsabar idanuwansa yana fada masa magana son ransa kamar wani wanda ya zo maula wajansa numfashi ya ja kafun ya dubi Dr.Erena sosai yana mai gyaɗa kai wani irin tukuki yake ji zuciyarsa nayi ba abin da yafi bata masa rai kamar yarda Dr.Erena ya zage yana keta masa rashin mutum bai taba tsammanin haka ba bai taba kawo wa kansa haka ba bai yi tunanin duk rashin mutuncin Dr.Erena zai iya yi masa. "Dr.Erena ni...". "I Say get out now i don wanna see you in my Office". Dr.Erena ya fadi a zafafe yana kara so wa wajansa har yana tunkuɗashi. "Ka je kayi abin duk da zakayi kudi ne na cinye in akwai wanda ya isa ya kwatar maka ka turo shi tunda naga abin naka hauka ne har nawa ne kudin naka da zaka zo kana yi mani ihu kamar wani kare a cikin Compay". Mamaki ne ya sake kume Alhaji Abdulwahaab jin zuciyarsa yake yi kamar zata faso kirji tayo waje gabadaya saboda tsabar tsananin bakin ciki dake nukurkusar sa hannunsa ya kai ya saukar da na Dr.Erena dake kafadarsa fuskarsa da wani murmushi kafin ya fara taka kafafuwansa a hankali har ya isa bakin kofar hannunsa saman Handle din ya juyo ya dubi Dr.Erena cikin wani irin kallon wanda shi kansa Dr.Erena sai da yaji wani iri a zuciyarsa amma bai bari hakan yayi tasiri a fuskarsa ba sai ma wata uwar harara da yake cilla masa. A daidai lokacin da ya tura kofar domin fita ita kuma Areefa ta sanyo kai cikin Office din saura ka dan suyi gware dashi amma tayi saurin kauce wa don a tunanin ta Dr.Erena ne. "Yaa Allah". Ta furta tana duban Alhaji Abdulwahaab da wani irin yanayi mai kama da tuhuma kafin ta dubi Dr.Erena da yake faman cika yana batsewa kamar zai tarwatse ganin Areefa ya sanya shi ware idanuwansa sosai mamaki na kokarin ka kashe shi ganin Areefa yau a cikin Office din sa How Comes yace ya manta rabon da ya ganta ko sashin sa ta zo amma yau ita ce a bangaren sa abin mamaki lokaci guda jikin sa ya shiga rawa ya fara takowa izuwa gareta a daidai lokacin ta juya ta dubi Alhaji Abdulwahaab yanayin da ta ganshi a aciki ya tabbatar mata akwai abin dake faruwa bata karasa tsinkewa da lamarin ba sai da ta ga Alhaji Abdulwahaab ya kashe mata idanu daya hakan ya kara jefata cikin wani irin yanayi mai girman gaske na mamaki. "Nace ka fice mani daga Office, ko sai na saka an fitar da kai a rashin mutunci ne?". Dr.Erena ya sake fadi a zafafe ganin irin kallon da Areefa ke yi masa juyawa yayi ya dube ta yana faman sakin Murmushi kamar tsohon da aka bashi kyautar budurwa. "Areefa ban yi zato ba...". Hannu ta daga masa alamun bata so fuskarta a tsuke. "Haba mana Dr.Erena me haka kayi wanda sam bai dace ba abokin ka ne fa wanda bai kamata ace irin haka ya faru a tsakaninku ba". Ta fadi tana mai dubansa kafin ta dubi Alhaji Abdulwahaab wanda a daidai lokacin yake ficewa daga Cikin Office idanu ta kashe masa kafin ta juyo da kallon ta zuwa wajan Dr.Erena fuskarta da alamun damuwa. "Ban san haka wasu in suka gani ai sai su yi muku dariya". Wani gundumeman tsaki ya ja gami da kau da kansa. "Bar ni kawai Areefa raina min hankali zai yi ni kuma a rayuwa ta abin da bana so kenan komin kusanci na da kai in har kace zakayi mani akuyanci to wallahi ba zan kyale ka". Sosai ta gano in da lamarin ya dosa amma cikin basarwa da kin ba wa zancen muhimmanci ta dube shi. "Good and Fine ina son mutum haka mai ra'ayi irin naka na rashin son daukar raini". Ai ji yayi kamar ta cilla shi a gidan aljanna haka ya shiga yashe baki kamar wani bugun shaho da sauri ya dube ta cikin rawar jiki yana yi mata nuna da ta zo ta zauna a hankali ta fara taka kafafuwanta idanuwanta na kansa kallon sa take yi da wani irin kiyayya mai girman gaske dubansa take yi da wani irin haushi da takaici zuciyarta take ji tana wani irin kartawa kamar zata faso kirjinta ta fito saboda tsabar tsanar sa da take ji a duk wani sashi na zuciyarta. 'Ni yake so wai da aure' Ta ji wani sashi na zuciyarta na fadin haka ji tayi kamar ta daura hannu aka ta kurma ihu don bakin ciki amma ina bata so ta bata shirinta ba ta so ta bata salon da Hajiya Layla ta karanta mata tayi amfani dashi bata so ta samu wata ɓaraka daga wannan KUDIRIN nata da take kokarin cin masa. Isa tayi cikin takunta wanda yake kara fizgar Dr.Erena yana jefashi cikin wani irin hali na matsanancin son ta sosai ya firgice cikin lokaci kalilan sai kai kawo yake yi yama rasa abin da ya dace yayi sai kai kawo yake yi yana dube-dube sannan ya juya ya janyo kujera kamar zai zauna sai kuma ya fasa ya shiga sakar mata murmushi ita kan ta sai da taji wani iri na daban da yanayin da yake nuna wa amma zuciyarta wani irin kunci take jefa ta a duk lokacin da ta kalle shi ji take yi kamar ta tashi ta shake shi ya mutu kowa ya huta sai dai wani sashi yana gargadin ta da wannan kudirin nata na kisa wanda sam bai dace ace tana sanyo shi a lissafin ta ba. "ka zauna mana gabadaya duk ka wani rikice sai kace wanda aka kama da satar butar masallaci". Sai a lokacin ya tsaya da kai kawon da yake yi ya janyo daya daga cikin kujerun dake girke a gaban Table din ya zauna yana fuskantar ta. "Nayi mamaki matuka da ganin ki Areefa na dauka har yanzu ba a yafe mani gingimeman laifin da nayo ba". "wa yace kayi laifi?". Ta tare shi tana mai sakin wani yake da BAI KAI ZUCI BA. "Uhmm dole nace haka mana Areefa yaushe rabon da ki tsaya ki saurare ni yaushe rabon da ko alfarmar kallon arzuki na samu a gareki muna Company daya amma har ki shigo ki gama abin da zaki yi ba ki dubana da kallon arzuki in ma nayi miki magana sai ki nemi dizga ni don kawai na nuna ina son ki ban san laifin da nayi har ya kai haka ba ban san me nayi miki da kika tsanani har haka". Runtse idanu tayi jin ya ambaci kalmar 'ina son ki' wani takaici da makakin bakin ciki taji sun taho sun tsaya mata a zuciya wani abu mai nauyin gaske taji ya zo saitin kirjinta ya zauna numfashin ta taji yana sama da kasa kamar zai katse. Sosai taji ba za ta iya cigaba da zama cikin Office din nan ba sosai take ba za iya kara ko da minti guda bane tare da Dr.Erena komai zai iya faruwa sosai zuciyarta ke tururi sosai take ji kwanyarta na juya wa. A hankali ta mike kan kafafuwan ta tana jin yarda kanta ke sarawa da wata irin tsana ta Dr.Erena bata zaton zata iya juri zuwa gareshi bata zaton zuciyarta za ta barta tayi abin da ya dace sosai take jin ina ma ace ta kashe shi shine kawai hanya guda da take zaton samun nasararta a akansa amma ina hakan sam bai dace ba bai dace ace zuwa wannan lokacin ace ta kashe shi ba ba ita kadai ke bukatar Dr.Erena ba ba ita kadai bane a filin duniyar nan take son daukar fansa akan sa mutane da yawa wanda ba ta san a dadin su ba suna BURI da KUDIRI mai girman gaske akansa sai dai rashin WATA DAMA da ba su samu ba amma gata ita ta samu amma tana kokarin ruguza komai. "Areefa ya dai ba dai tafiya zakiyi ba?". Muryar Dr.Erena ta doki kunniwanta ba ta san ma ta fara tafiya ba sai da taji amonsa sanna ta dawo hayyacinta har ta kai bakin kofa da sauri ta juya ta dube shi fuskarta da wani irin murmushi wanda ita a karan kanta ba ta san ma tayi ba sam! ba tare da tace dashi komai ba ta buɗe kofar ta fita. Fitar ta ke da wuya Dr.Erena ya mike cikin hanzari fuskarsa na kara haɗewa waje guda wayarsa ya janyo ya shiga danna kira yana mai kaita saitin kunnuwansa sai faman numfashi yake ja. "Bobby". Ya fadi da wata irin murya kafun ya dora da fadin. "Ina son ganin ku anjima a gida". Daga nan bai sake cewa komai ba ya sauke wayar yana mai sakin wani murmushi na mugunta yana murza gashin gemunsa. "Alhaji Abdulwahaab". Ya furta yana mai hade hannayensa waje guda yana lankwasawa. ****** "Meye amfanin haka da kayi Alhaji Abdulwahaab baka tsoron Dr.Erena ya turo a kashe ka don karka kawo masa tsaiko cikin lamarin sa kai fa da kanka ka fadi mani ko waye ya zo masa da rainin hankali ko yana kokarin tona masa asiri kashe shi yake yi amma kai kayi gangancin tunkaransa akan wani dalilin?". Areefa ta fadi tana mai duban Alhaji Abdulwahaab da takaicin duniya ya ishe shi sai faman huci yake yi kamar wanda zai hadiyi zuciya ya mutu. Mikewa yayi tsaye ya shiga kai kawo sai faman kai wa iska naushi yake yi kamar da ita cikin wanda suka bata masa rai juyawa yayi ya dubi Areefa ita ma idanuwanta na kansa hannun ta rike da Glass Cup a hankali take kurbar lemon da yake ciki. "Areefa ya kamata ki san wani abu wannan abin da ki ga nayi masa so nake yi na kara tunatar dashi cewar ina nan fa ban matan abin da ke tsakaninmu ba don na lura sam ya mance wani abu da ya shiga tsakanina dashi ba wai nayi bane don neman hakki akan sa a,a nasan ma ba samu zan yi ba nayi hakan ne don ya sani ina nan kuma komai daren dadewa sai ya bani hakki ba zai ci bulus ba". "Wannan ba magana bace Alhaji Abdulwahaab". Areefa ta katse shi da fadin haka kafun ta dora da cewa. "Ko Shakka bana yi yanzu haka nasan yana nan ya na kokarin bin hanyar da zai kawar da kai a filin duniyar nan kar kayi tunanin ABOTA da ta ratsa tsakaninku zatayi wani tasiri a gareshi na rantse maka da Allah yarda da lura da Dr.Erena duk da dai kafi ni saninsa amma ina da zaton ko kaninsa ne zai kawo masa wasa zai iyayi masa komai Dr.Erena MUGUN ABOKI ne a gareka domin kuwa ba ya bukatar ace ka samu cigaba yarda yake yi maka yana nuni da cewa da ma can abin ka yake so". Runtse idanu yayi yana kai komo zuciyarsa yake ji tana zafi bai taba zaton Dr.Erena zai masa haka ba bai taba zaton ko da a mafarki ne haka zata faru ba. "Shikenan Areefa amma don Allah ya kamata ace zuwa yanzu kin san komai game dashi lokaci tafiya yake yi a ko wani lokaci zai iya gano ke wacece tsoron abin da zai je ya dawo bana so ayi BIYU BABU ba wan ba kanin karatun dan kama". Wani murmushi ta saki kafun ta juya idanuwanta. "Alhaji Abdulwahaab". Ta fadi cikin wani irin yanayi tana mikewa kan kafafuwanta da wani irin ƙarfi da take ji yana taso mata tun daga zuciya da rushi ajiya Cup din dake hannunta tayi kafin ta dauki jakarta dake kan Table din da suke zaune a hankali ta fara taku kamar ba zata ce dashi komai ba juyawa tayi a hankali har zuwa lokacin da murmushi a fuskarta da BAI KAI ZUCI BA amma yana tattare da abubuwa masu yawa. "Yanzu za a fara Alhaji Abdulwahaab ka shirya zaman kallo". Ta fadi tana mai kashe masa idanu kafin ta juya ta cigaba da tafiyarta cikin sassarfa. Hannu ya daga ya jinjina mata yana hango gaskiya a batunta yana hango kudiri da buri da ta dauka akan Dre.Erena abin da yake so kenan dama kuma tsaf ya shirya duk yanayi sai ya ga yarda wasan nan zai kare kamar yarda ta fada amma kuma dole ya ja baya da Dr.Erena kamar yarda Areefa ta fadi ya san dole ya farauce shi a ko wani yanayi zai iya yi masa bazata. ******* Kai kawo kawai take yi cikin tsakiyar falon gabadaya kanta ya gama kullewa tunaninta take ji ya cak! ya daina tafiya yarda ya kamata numfashi take ja a hankali tana dukan hannunta da dayan idanuwanta sun kaɗa sun yi jajir kallo daya zakayi mata ka gane tana cikin damuwa matsananciya da tarin KALUBALE. Sosai take ji a ranta lokaci yayi sosai take jin komai na dawo mata kamar yarda ya faru a shekarun bayan komai zuwa mata yake yi komai kallon sa take yi a yanzu yake faruwa ba TUNA BAYA bane runtse idanuwanta tayi zuciyarta da wani raɗaɗi da zugi ga wani bugu da take yi kamar zata faso kirji ta yo waje. Zubewa tayi kan kujera ta mai jan numfashi wasu kwalla suka cika mata idanuwa hannun bibbiyu ta dafe kanta da take ji yana barazanar tarwatsewa. "Yaa Allah". Ta furta cikin wani irin yanayi matsananci duniyar take ji tayi mata zafi da kunci komai take ji babu dadi a hankali ta kuma mikewa hannayenta goye a bayanta ta cigaba da safa da marwa so take yi ta tunano abin da ya dace tayi so take yi zuciyarta ta kawo mata wata satar ansa da za tayi mata amfani so take yi kwanyarta ta binciko mata wani abu mai girman gaske da ya dace ace shi ya kamata tayi. Motsin kofar da taji ne ya sanyata saurin juyawa Areefa ce ta gani tana kokarin shigowa cak! ta tsayar da idanuwanta akan ta sosai take jin komai na sake dawowa mata kamar yanzu ya faru wani tunani taji ya zo mata a bazata runtse idanu tayi tana mai sake buɗe su akan Areefa gabatan taji yayi wani irin dokawa da abu mai girma. 'Anya kuwa?' Ta fadi a can cikin ranta tana mai girgiza kai a daidai lokacin Areefa ta iso gareta tana mai dubanta. "Ya dai Maama ko jikin ne?". Ta fadi tana mai yawatawa da idanuwanta akanta. Girgiza ka tayi alamun babu komai hannunta ta riko tana mai sarkewa cikin nata da wani irin yanayi mai girman gaske da sauri Areefa ta bude idanuwanta tana kallon cikin yanayi na alamun son sanin wani abu murmushi tayi mata kafun ta jata suka zauna waje daya suna fuskartar juna zuciyar Areefa sai kai kawo take yi so take yi ta san abin da ke faruwa domin ta hakiƙance yanayin da take ganin Hajiya Layla a ciki ya tabbatar mata akwai matsala bata saba ganinta cikin wannan yanayin ba duk da boyewar da take yi na abin dake damunta amma ita a jikinta taji kamar akwai wani abu mara dadi dake shirin faruwa. A hankali ta shiga motsa laɓɓanta idanuwanta akan Hajiya Layla da sai faman yak'e take yi kamar wacce akayi wa dole zuciyarta na bugawa da wani irin yanayi na tashin hankali tsoro take ji tsoro mai girman gaske tana son tayi wa Areefa magana amma zuciyarta na gargadinta akan haka bata san ya zata dauki lamarin ba bata san ya zata fuskata ba tsoronta daya lamari ya maimaita kansa bata son haka bata son abin da zai sake dawowa a matsayin WAIWAYE sosai ta sani Areefa zata tashi hankalinta ita kuwa a filin duniyar nan abin da ta tsana kuma take gudunsa kamar shiga damuwar Areefa bata so ace ta sanadinta wani abu ya same ta so take yi ace har karshen rayuwarta ta dauwamar da Areefa cikin farinciki da muradan jin dadi amma Ta ya ya hakan zata kasance?. 'Bata sani ba'. Zuciyarta ta fadi duban Areefa tayi akaro na ba a dadi wacce gabadaya ta gama shiga yanayi lokaci guda jikinta yayi sanyi sosai. "Maama wai meke faruwa ne don Allah sosai naji gabana na faduwa fa don Allah fada min". Ta fadi tana mai kara matse hannunta a na Hajiya Layla. "Ban san ya zance miki ba, ban san ta ya ya zan fuskance ki ba, sosai nake jin rashin jindadi sosai zuciyata ke bugawa ina tsoron abin da zai je ya dawo, ba na son ace ta sanadina kin sake fadawa halin damuwa bana so nayi miki Waiwaye...". "Maama!!!". Areefa ta fadi da sauti mai girma a muryarta kafun ta sake motsa laɓɓanta kamar zata yi kuka. "Don Allah mene ne? Ki fada min zuciyata sosai take bugawa Allah taba ki ji". Ta karashe tana mai dago hannun Hajiya Layla tana kaiwa saitin inda take zaton zuciya na ajje. "Areefa wani abu nake so na tambaye ki guda daya kwal! Amma kuma ban san yarda zaki dauki lamarin ba ban san da wacce fuska zaki anshe ni ba...". "Kawai ki fadi koma mene ne zan dauke shi a yarda ya zo mani nayi miki alkawari". Ta fadi da murmushi na kara karfin gwuiwa ga Hajiya Layla don ta lura da ita sosai yanayin ta ya sauya kamar da tsoro akan abin da take so tambayar ta akai. "Zaki iya tuna ranar da muka dauko ki daga gidan marayu?". Yanayin da take furta kalmomin da yarda bugun zuciyarta ke sauyawa ya sanya Areefa kureta da idanuwa kanta taji lokaci guda ya ansa wata kara mai girman gaske kirjinta yayi wani irin dokawa kamar zuciyarta zata faso kirji ta fito a hankali ta ji duniyar na juya mata idanuwanta lokaci guda suka shiga lumshewa da wani irin tashin hankali mai girma wani CIWON RAI mai tsanani zafi da zugi taji ya ta so mata komai taji yana dawo mata kamar yanzu yake faruwa gabadaya numfashin ta ya dauke lokaci guda ta zube jikin Hajiya Layla ganin haka da ita kuma tayi ya sanyata kwala kara mai sautin sai da falon ya ansa gabadaya cikin tsananin firgici da razana tashiga girgizata tana ambatar sunanta amma ina Areefa tayi nisa cikin wata duniya mai cike da kwazazzaben tashin hankali da sanya zuciya ciwo. Da gudu ta mike ta isa wajan Firjin dake girke cikin falon ta buɗe gorar ruwan EVA ta sungoma tana mai balle murfin tana isowa gareta ta tuntule mata akai aiko wani numfashi mai karfi ta ja har tana sarkewa da sauri Hajiya Layla ta durkushe idanuwanta na zubda hawaye masu zafi jikin ta ba abin da yake yi sai rawa laɓɓanta na kaɗawa. "kiyi Hakuri Areefa ban so haka ba, abin da nake gudu kenan shiyasa na ki tambayar ki ban son abin da zai jefa rayuwarki a wani yanayi ban son na sake fama miki ciwon da ya jima a zuciyarki...". Cikin wani irin yanayi Areefa ta daga mata hannu. "Bakomai Maama wallahi ba komai karki damu tambaye ni abin da kike bukata na san ba wai zaki tambayeni bane don cutar dani". Ta fadi da hawaye a idanuwanta zuciyarta na wani irin motsawa da ciwo mai tsananin gaske laɓɓanta take tura cikin bakinta tana cizawa komai taji ya sauya mata jikinta take ji yana narkewa kamar ruwa. Duban Hajiya Layla tayi wacce gabadaya ta gama rikicewa da tashin hankali ganin halin da Areefa ta shiga jikinta sai faman kaɗawa yake yi ta janyota jiki tana rungumewa. "Kiyi Hakuri Areefa...". "Ya isa haka Maama don Allah". Shiru tayi jin abin da ta fadi dubanta take yi cikin wani irin yanayi na tausayawa zuciyarta na kara narkewa da kauna da tausayin Areefa. "Shikenan na bari". Hajiya Layla ta fadi da murmushin yake a fuskarta Kafun ta riko hannun Areefa sosai tana kwanta da kanta a kafadarta. "Abu daya nake so ki fama min in har zaki iya tunawa Areefa kuma in har ba za ki kuma shiga yanayin nan da kika shiga yanzu ba kiyi man alkawari". Gyaɗa kai tayi da murmushi a fuskarta tana mai kara kwantar da kanta a kafadar Hajiya Layla. "NAYI ALKAWARI". Shiru ne ya ratsa falon na yan mintina ba wanda ya sake magana a cikin su sai ajiyar zuciya kawai a hankali Hajiya Layla take shafar kan Areefa tana son yin magana amma zuciyarta na tsoratar da ita akan yin maganar domin bata san abin da zai faruwa ba sai dai kuma bata da zaɓi dole sai tayi tambayar domin ita kadai ce hanyar da take hango mafita a gareta da ita kan ta Areefa din. "Bayan fita ta daga cikin Motar Dr.Erena shin gidan sa kuka tafi ko kun biya wani waje daban ne?". Tsoro sosai ya bayyana a fuskarta lokacin da take maganar tana jin yarda jikin Areefa ya dauki rawa lokaci guda tana kankameta ajikinta sosai taji wani irin yanayi wanda bata san ya zata misaltashi ba game da Areefa lokaci guda taji gabanta ya yanke ya fadi da tashin hankali. "Areefa". Ta kirata muryarta na rawa. "Na'am Maama". Ta ansa ta da son nuna ba komai amma yarda take ji a zuciyarta da ruhin ta kamar an dauko KASKO WUTA an juye mata haka take jin kirjin ta na wani azabar zafi runtse idanu tayi kafun ta motsa baki. "Ba gidansa muka je ba wani daji muka nausa sosai ya kaini wani gida wanda shi kadai ne a wannan lokacin...". Da hanzari Hajiya Layla ta dagata tana dubanta bakinta har rawa yake yi. "Kenan ba gidan sa ya kai ki ba ko to gidan da kike ce kun je din waye a cikinsa?". Runtse idanu ta sake yi idanuwanta na kawo kwalla. "Haba mana Areefa karki yi kuka kin yi mani alkawari". Hannu ta saka ta dauke hawayenta kafun ta shiga bata labrin abin da ya faru shekaru masu dama da suka shuɗe. Kuka sosai Hajiya Layla take yi zuciyarta da ruhinta na zafi sosai ta rungumi Areefa ita ma da take kuka a hankali ta mike fuskata da murmushi mai tsananin ciwo. "Shikenan Areefa ina so duk runtsi duk wuya karki sake daidai da rana daya Dr.Erena ya san nan gidan sannan ko yace yana so ya gana da iyayenki kice masa zakiyi shawara ki zo ki same ni don nasan nan da dan lokaci ya bukaci son ganin iyayenki domin neman auren ki auren da nake so ayi sa...". "Maama". "Shiru Areefa kiyi abin da nace kawai". Daga nan ba wanda ya sake magana a cikin su Hajiya Layla sai safa da marwa take yi a tsakar dakin ita kuwa Areefa kwance tayi luf! tana jin yarda tsana da kiyayyar Dr.Erena ke kara samun masauki a filin zuciyarta KUDIRI tayi tare da Alkawari duk runtse sai taga bayan sa a filin duniyar nan.. *_KAMALA MINNA_*😘😘 [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA TALATIN DA BIYU Zuciyarta take ji tana yi mata nauyi, da abu mai girman gaske. komai take ji yana zama kamar tarihi gani take yi kamar ba ta kwashe wadannan shekarun da suka bawa rayuwarta baya ba wai ita ce yau ta gama makaranta wai ita ce yau ake bikin kammala makarantar su, a matakin sakandire. gani komai take yi kamar ba gaske ba, gani takeyi tamkar mafarki ne take yin sa wanda a ko wani lokaci zata iya farkawa. A hankali ta kai yan yatsunan Hannunta na dama zuwa bakinta tana cizawa, kamar zata zare su daga jikinta komai take ji yana tabbatuwa, komai take ji yana gasgatuwa, komai take ji yana zama zahiri ba badini ba. runtse idanuwanta tayi tana mai buɗewa ta shiga yawatawa da idanunta zuwa harabar makarantar dalibai birjin kowa sai murna yake yi da farinciki fuskokin su dauke da tsananin farin ciki mara gushewa. 'Yaa Allah'. Ta furta cikin wani irin yanayi mai girman gaske zuciyarta take ji tana buɗewa sosai tana haifar mata da wani lamari mai girman gaske kwanyarta take ji ta shiga shawagi da ita cikin wata irin duniya na farinciki sosai take jin duk wata gaɓa ta jikinta tana ansa sakon da zuciya da ruhi suke miko musu na farin cikin da take ciki a yau din nan. "Wayyo Allah na. Mariya gabadaya na gaji wallahi". Muryar Baseera ce ta doki dodon kunnuwanta da sauri ta dago kai tana dubanta tana mai sakin yak'e gami da gyaɗa ma kai. Kuri Baseera tayi mata da idanu kamar mai son gano wani abu daban a hankali ta shiga janye hannayenta data dafa kafadun Mariya idanuwan na kara yo waje da yanayi na damuwa ba bacin rai. "Meye haka Mariya, me fuskarki ke kokarin nuna min ba dai zaki ce mani ba kya farin ciki da wannan ranar ba Yaa Allah!". Ta karashe tana mai dafe kanta da take ji yana sara mata da wani irin yanayi mai girma da tashin hankali a cikinsa runtse idanu tayi kafun ta buɗe su kan Mariya da tayi shiru idanuwanta da wani yanayi na damuwa a ciki. "Ban san me zan ce miki ba kuma Mariya, Shekaru fa tafiya suke yi kamar gudun ruwa a kogi ya kamata ace wannan shekarun da kika shafe kin canza komai a duniyarki, ki duba ki gani kin canza tsarin ki ya canza ke kan ki kin san komai game dake ya sauya sai dai abu daya...". Tayi shiru tana jan numfashi mai dauke da damuwa mai girman gaske kau da kai tayi daga barin kallon Mariya ta juya kan dalibai dake ta fara'a da farin ciki. "...Zuciyarki Mariya taki sauyawa, komai ya ki canzawa a cikinta kin ki baiwa rayuwarki damar kawo maki farin ciki a filin duniyarki Ban san mai ya sa ba?". Sake kusantowa tayi gareta tana dafa kafadarta. "ki na tunanin rayuwa zata yuwu a hakan kina tunanin wanan tsarin da ki daukar wa kan ki zai haifar miki da ɗa mai ido a rayuwarki ina! haka ba zai taba yuwuwa ba ya kamata ace kin sauya Mariya ki sauya rayuwarki!!!". Ta karashe cikin murya mai amo da sauti tana rike kafadun ta tana girgizawa har sai da mafiya yawan dalibai suka dube su sosai. Runtse idanu Mariya tayi tana mai toshe kunnuwanta da hannu bibbiyu lokaci guda idanuwanta suka kaɗa sukayi jajir jikinta lokaci guda ya shiga rawa kamar wanda ruwa yayi mata duka sosai da sosai a hankali take duban Baseera da idanunta bakin ta na faman rawa kafin ta ciji laɓɓanta tana jin yarda zuciyarta ke matsewa a waje daya da girman damuwar da take ciki. "Ban san ya zan yi ba Baseera, komai da komai duniyar ma gabadaya ta canza ban san haka duniyar take ba da ban so na shigo ta ba da na roki Allah ya barni a wata duniyar ba wannan ba zuciyarta ta gaji Baseera sosai zuciyata take zafi ban san meye maganinta ba kullum kullum komai kara rikice mani yake yi". Ta karashe wasu zafafan hawaye na zubowa a fuskarta kafin ta sanya hannayenta ta dauke su. "Mu tafi gida Baseera". Mariya ta fadi tana mai shigar da hannun Baseera cikin nata tana jan ta ba tayi mata kardama ba haka tabi ta kamar rakumi da akala kawai binta take yi da idanu cikin wani irin yanayi zuciyarta sai faman dokawa take yi da lamarin Mariya bata san inda rayuwar Mariya ta dosa ba sosai komai da komai ya fita daban a rayuwarta tana matukar tausaya mata musamman yarda Kuruciyarta ta kasance da tashin hankali wanda ta rasa gane in da ya dosa a filin duniyar nan. "Ba muyi Sallama da kowa ba Mariya hakan bai kyautu ba". Baseera ta fadi cikin rashin abin yi tana faman jan numfashi. Cak! ta tsaya Daga tafiyar da take yi kafun ta juyo ta dube Baseera suka fuskanci juna sosai idanuwansu na yawatawa a tsakani gyaɗa kai Mariya tayi kafun ta sake kallon filin makarantar da yarda dalibai suke kai komo. "Ba abin da yayi saura da za mu tsaya muma kai kawo akan sa ban zan iya cigaba da zama bane na fi bukatar na je gida". Kallon ta take yi da duk yanayin da take magana dashi da sam ba wani abun na a zo a gani murmushi take sakar mata na karfafa gwuiwa don bata so ta karyarwa da Mariya zuciya. "Shikenan naji mu tafi gidan amma da kin bari Dadyna ya turo a dauke mu bari na kirasa". Ta fadi tana mai zuge tsakarta domin dauko wayarta da sauri Mariya ta tare ta. "Barshi ba sai kin kira shi ba kawai mu tafi domin a hanya zamu rabu gida zan wuce daga nan". Ware idanu tayi kadan cike da mamaki. "Ba zaki je gidan namu b...". "Kawai dai zan zo amma yanzu na fi bukatar naje gida bana tattare da natsuwa a filin rayuwata". Gyaɗa kai Baseera ta shiga yi kamar wata kadangaruwa a hankali ta fara taka kafafuwanta tana karasawa bakin titin dake kusa da Get din makarantar ta su. Bata son ta matsawa rayuwar Mariya bata so ta fiye yi mata magama akan abin da ta san ba ranar karewarsa komai take gani a filin duniyar mariya sai kara rikicewa yake yi sosai take jin tausayinta a zuciyarta da ruhinta sosai ita a karan kanta tana jin rashin jindadi a rayuwar ta ba macen da ta dauko a matsayin yar uwa ba ƙawa ba kamar Mariya sosai take jin sashi na zuciya da gangar jikinta na sauyawa da duk wata damuwa ta Mariya. Nisawa tayi kafun ta daga hannu tana mai tsaida mai Napep bayan ya tsaya ta kira Mariya dake can gefe guda ta zo su ka hau domin wucewa. Ko a cikin Napep ba wanda ya yi magana kamar mutuwa ta gifta su cikin yan mintina kalilan suka isa layin su Baseera nan ta sauka ta biya mai Napep kudinsa har da na Mariya da zai kai ta gidan su. "Mariya sai na zo ki gaida su Umma". Gyaɗa mata kai tayi tana mai sakin yak'e nan mai Napep ya dau hanya domin isa da Mariya gida. **** A hankali take takawa ko ina sasan jikin ta motsawa yakeyi sanye take da doguwar riga mai kalar baki da fari sa mayafin da tayafa kalar ja fuskarta da saukakkiyar kwalliya laɓɓanta sun yi jajir dalilin jan bakin da ta saka ja mai turuwa tun daga kofar gida take kallonsa da wani irin yanayi mai girman gaske tana faman sakin wani murmushi mai kayatarwa a haka har ta iso gareshi. Jingine yake da motarsa ya harɗe hannayensa a kirjinsa idanuwansa kur! Akanta kamar ya ga sabuwar halitta a filin duniyar sa. Sosai yaji gabansa yayi wani irin dokawa lokaci guda rintse idanuwansa yayi cikin tsananin tashin hankali mai girman gaske a hankali ya shiga buɗe su yana saukewa akan ta a daidai lokacin da ta iso gareshi cikin takun ta na jan hankali kusa dashi ta tsaya tana mai sanya hannunta guda tana dafa jikin motar sosai ta fuskance shi tana mai kaɗa idanuwanta cikin salon jan hankali. "Uhmm Huzaif ai ban yi tunanin zaka zo ba". Ta fadi tana mai kai hannayenta tana kara gyara zaman mayafin nata wanda a zahirin gaskiya ba wai tayi bane da sunan gyarawa a,a kawai tayi ne domin ta bayyanar da yarda rigar tayi matukar matse ta a kirji haka ya kara bayyanar da cikar kirjin nata na matashiyar budurwa mai ji da kanta. Murmushin yake kawai yake saki kafun yaja numfashi. "Eh wallahi amma... Nace ba...". Sai kuma yayi shiru yana mai dubanta idanuwanta da ta kafe sa da su sosai yake hango wani irin yanayi da yake narkar masa da duk wani sashi na jikinsa bai san abin da ya hadashi da Hafsat ba bai san ya akayi ta shigo filin duniyarsa ba bai san ya aka yi har yake tsaye suna magana ba sosai zuciyarsa ta buga a duk lokacin da ya ga Hafsat a gabansa komai da yake kwanyarsa da zuciyarsa canzawa yake yi sosai yake jin filin duniyarsa na canzawa game da ita. "Kayi magana mana Huzaif". Ta fadi cikin salon kashe murya sai faman juya idanuwanta take yi a nasa. "Uhmm ba komai wai dama cewa nayi Mariya ta dawo?". Ya fadi cikin yanayi na ɗarɗar kamar wanda yayi laifi ake tuhumarsa. Ware idanu tayi jin abinda ya fadi ta shiga tsuke fuska kamar biri da lemon tsami. "Me kake nufi Huzaif me ya kawo Mariya a maganar mu meye kuma hadin ka da ita na dauko ba wata 'ya mace a filin rayuwar ka a yanzu kamar ni wacece Mariya kuma?". Ta fadi cikin sauti kamar zata kai masa bugu kafun lokaci daya ta rikice da zubda hawaye tana shassheka. Hakan ba karamin firgita Huzaif yayi ba da sauri ya shiga ba ta hakuri kamar zai yi mata sujjada jikinsa ba abin da yake sai ɓari da kakarwa a hankali ya zaro Hankicif a aljihunsa ya kai fuskarsa cikin rawar jiki yana dauke hawayen. A daidai lokacin kuma Mai Napep yayi Parking Mariya da take ciki tana kokarin fitowa ta hango su wani irin bugu taji gabanta yayi kanta ya shiga juyawa kamar zata zube a kasa da sauri ta rike karfen kofar Napep din tana ambatar. "Yaa Allah". Komawa tayi ta zauna idanuwanta a runtse tana jin yarda zuciyarta ke yayyakewa da tashin hankali mai girman gaske ba ta san lamarin su ya kai har haka ba bata san cin amanar har ya kai haka ba ta lura So suke yi su ga bayanta so suke yi su kashe ta da ranta ba ta san sai yaushe zata daina ganin wannan bakin lamarin ba ba ta san sai yaushe duniyarta zata canza yanayi. Sosai take cikin tashin hankali mai girma gaske mai kokarin raba ta da duk wani farin cikin da yayi saura a filin duniyar...ko da yake ba ma zata ce akwai farinciki a cikin duniyarta ba a yanzu domin ya jima da gushewa shekaru uku ana abu daya zuciyarta kullum cikin ciwo take sosai take hango yarda ALKALAMIN ƘADDARA yake juya duk wata rayuwarta a duk sakan ba ta tsammanin a cikin shekaru uku da suka bada baya daidai da rana daya ta samu farinciki bata tunanin a cikin shekaru uku da suka shuɗe daidai da minti daya tayi dariya wai ta farinciki ba ta san wacce irin rayuwa bace take yi a duniyar nan komai da komai nata na daban ne bata tsammanin a duniyar nan akwai mai rashin jindadi da kwanciyar hankali kamarta. Numfashi ta ja mai karfi zuciyarta na dauko mata jarumta tana aza mata ta gaji ba zata iya cigaba da zubda hawaye akan mutanan da ba su san tana yi ba ba za ta kashe rayuwarta akan mutanan da ba su san darajar da kimarta ba ta daina damun kan ta ta daina sanya kaita a damuwa alkawari tayi daga yau ba wani daga cikin su da zai sake dasa mata ciwo a zuciya buɗe idanuwanta tayi a hankali ta saka hannayenta ta shafe kwallar da suka cicciko mata fitowa tayi daga cikin Napep ta dube mai Napep wanda yayi kuri yana kallonta ganin ta fito ya buɗe bakin sannan cikin yanayi na tausayawa don ya tabbata akwai abin da yake dawainiya da duniyar rayuwarta. "Sai Hakuri yan mata lamarin duniya ne sai an din ga kai zuciya nesa". Gyaɗa kai kawai tayi tana mai sakin yaƙe wanda take jin sa har cikin zuciyarta da sauri ta janyo hijabin jikinta ya dan rufe mata fuska cikin yanayi na hanzari ta doshi kofar gidan domin bata so ma su ganta balle wani cikinsu ya raina mata hankali... "Mariya!". Kamar daga sama ta jiyo sautin muryarsa ya ambace ta cak! Ta ji ta tsaya da tafiyar da take yi sosai ta ji sautin amon muryarsa ya ansa kuwwa a kunnuwanta da ma kwanyarta bakidaya a hankali ta dago kanta jin sautin takunsa yana karaso wa in da take kallo daya tayi masa da kai jin yarda zuciyarta ta harba da wani irin yanayi mai ciwo sosai. "Uhmm...". Da sauri ta dago kai gami da daga masa hannu lokaci guda idanuwanta suka kara rinewa fuskarta kamar hadari da yake kokarin zubda ruwa. "Huzaif!". Ta ambata cikin muryar gargadi kafun tayi masa wani irin duba wanda shi akaran kansa sai da yaji a jikinsa. "kana tunanin a filin duniyar na akwai KALMA DAYA da zaka fadi na tsaya na saurareka akanta kana tunanin akwai lokacin da zan iya batawa akan ka". Wani murmushi ta saki kafun ta juya ta dubi Hafsat dake tsaye jikin motarsa sai fama cika take yi tana batsewa. "Bana tunanin akwai wani abu yayi saura a tsakanina da kai na fadi maka ba sau daya ba ba sau biyu bs hanyarmu ta rabu ba zamu sake haduwa ba har abada ya kama ta ka san da haka amma na lura so kake yi ka ture lamari kaki dauƙarsa da muhimmanci ka sani ba yarda za ayi kana tare da yar uwata sannan kace kana tare dani ta ya ya wannan lamarin zai kasance ina so ka sani ni da kai ba wata ALAƘA da za ta sake shiga tsakaninmu don haka na rokake da ka fice mani a rayuwa Huzaif na rokeka daga yau...". Shiru tayi jin yarda zuciyarta tayi wani irin nauyi mai girman gaske kasa tayi da kanta tana jin yarda idanuwanta ke raɗaɗi da kokarin zubda kwalla da sauri ta bar wajan tana karasawa cikin gida. Bin ta yayi da sauri yana kiranta amma ina sai ma ta kwasa da gudu ta fada cikin gidan cak! Ya tsaya bakin soron yana mai da numfashi da yake ji yana kai kawo kamar zai rabu da gangar jikinsa hannayensa duk biyu ya dafe kan sa da su ji yake yi duniyar gabadaya na juya masa da wani irin ta shin hankali mai girman gaske bai san abin da yasa Mariya take gudunsa ba bai san abin da yayi mata ba baya iya tuna komai komai yake ji yana sauya a filin duniyarsa daga kansa yayi ya dubi Hafsat da tayi masa kuri da idanu sai faman kumbure kumbure take yi cikin hanzari ta baro jikin motar ta tun karoshi kamar wacce zata kifa. "Huzaif ni zaka ci wa zarafi ni zaka wulakanta a gaban waccen karamar yar duniyar ni zaka ketawa mutunci a gabanta to billahillazi baka isa ba zaka san ni kayi wa haka ka saurare ni". Ta karashe tana mai jan tsaki kamar zata tsinke Harshenta. "Hafsat mana! ki daina fadin haka ni ban ci miki mutunci ba sannan ban ci zarafin ki ba". Wani kallo ta yi masa tana mai sake narkar da muryar cikin yanayi kamar mai son sakin kuka. "Haba mana Huzaif ya za ace a gaban makiyiya ta zaka tsaya kana kulata ai sai ta rainani gaskiya ni karka sake in kuma ba haka komai zai iya faruwa". "Naji shikenan ba za a kuma ba". ko dubansa ba ta sake yi ba domin kuwa taji haushi matuka da yanayin da ta ga ya tsaya da Mariya a hankali ta ja kafafuwanta ta shige cikin gida shi kuwa Huzaif nan ta barshi tallaɓe da kai yana jin duniyar na juya masa ji yake komai na kwance masa a hankali ya ja jiki ya isa wajan motarsa ya shiga sai da ya shafe lokaci kafun yayi mata Key ya bar unguwar. ******* Kallon da Umma ta watsa mata ne ya sanyata saurin yin kasa da kai tana kokarin shigewa daki ta dakatar da ita. "Zo nan Mariya". Duban Umma tayi ganin ba wasa a fuskarta ya sanyata dawowa da baya ta samu waje ta zauna. "Baki ji ko Mariya, baki dai ji ko ni ban isa dake ba, ban isa nace miki bana son abu ba ko, ke kenan kullum abu daya kamar cin kwan makauniya dube ki don Allah kullum jiya i yau kowa na auki da kuzari amma ban dake kamar wata kazar mayu ban san ya zan yi dake ba ban san mai zan miki ba kuma ni dai a gaskiya na gaji da wannan lamarin naki na lura dai so kike yi ki kashe kan ki sannan hankalin zai kwanta in ba haka ba ta ya ya mutum sam shi a rayuwarsa ba zai dauki ƙaddara da jarabawa ba". Yanayin da taji sautin Muryar Umma ya tabbatar mata yau dai ta kaita karshe duk hakurin Umma yau tayi mata fada tabbas abin ya kai intaha runtse idanuwanta tayi ta sani Umma ta dade cikin damuwa da ta ta damuwar ta sani sosai lamarin ta yake damun Umma sosai take gani a yanayinta tsayin lokacin da ta dauka cikin wannan halin ita ma haka ne ya kasance wasu hawaye taji sun zo mata. "In kika sake kikayi mani kuka a nan wallahi sai na kwada miki Mariya don naga lamarin naki ba sauki sai abu ya ki ci yaki cinyewa haba mana maza ki tashi ki bani waje nikam tun kafin ki kai ni Bango ance mutum ya girma amma sam rayuwarsa ba ta sauya ba". Da sauri ta dago idanuwanta da suka cika da kwalla ta sanya hannu ta dauke su. "Uhmm Umma fa ba wani abu bane ba abin da kike zargi bane fa kawai bana jin dadin jiki nane kisan yau muka kammala komai na makaranta daga yaushi kenan". Kuri tayi mata da idanu tana karantar yanayin ta ta san Mariya ba za tayi mata karya ba kuma in har bata manta ba kwanakin baya ta sanar da ita sun kusan kammala karatun nasu gyaɗa kai tayi tana mai sakin fuska sosai. "Yo ai ke ce Mariya wani lokacin da kayan haushi kike wallahi sam ba a gane miki yarda kika san sahun keke ai shikenan Allah ya taimaka yasa anyi a sa'a kin ga yanzu dai burin naki ya fara ciki sai ki zage kuma ki cigaba da kokari kamar yarda kika saba". Gyada kai tayi tana mai kalato murmushi tana daura a fuska mikewa tayi. "Yawwa na mance dazu ma Yayan naki ya kira ni a waya". Ras! Gaban ta ya fadk da sauri ta juyo ta dubi Umma cikin yanayi na tsoro. "ya tambaya ina kike nace kina makarantar wai shi ne yace har yanzu baki kammala ba ne ya dauko tun wacce shekarar ai zaki gama". Yaƙe tayi. "Ke ma dai Umma tun yaushe nace miki mun gama kawai mun dau shekara daya mun kara domin koyan sana'o'i hannu ke fa nan na fada miki an buɗe makarantar koyan sana'a na fada miki kuma kika aminci amma yanzu kina nuna ba ki sani ba". Dafe kai Umma tayi kafun ta dubi Mariya. "Wai ni kam anya ban da cutar mantuwa kuwa Mariya haka fa mukayi da Yayan naki shekaran jiya wallahi yace an kawo sako nace a,a bayan kuma an kawo din". Murmushi Mariya tayi. "Akwai abin da kika sakawa ranki Umma". "Ai komai ya faru kece sila mariya lamarin naki ne sosai ya firgita min rayuwa komai nawa sai a hankali...Allah dai ya kyauta kawai". "Ameen Yaa Rabbi". Mariya ta ansa tana mai shigewa daki zuciyarta da wani irin yanayi mai girman gaske ba abun da ke ansa kuwwa sai maganar Umma nacewa Dr.Karami ya kira wai har ya tambayeta abin ya daure mata kai in har bata manta ba yau kusan shekaru hudu kenan rabonta dashi duk zuwan da yake ba sa haduwa kullum cikin wasan buya suke a tsakanin su ta rasa dalilin da yasa haka ta rasa mai ya ke damun Dr.Karami komai nashi ya sauya tunda ya dauki kafarsa ya bar kasar nan shikenan kuma ya shafe babin ta da farko ta dauka laifinta amma daga baya kuma zuciyarta ta jima tana sanar da ita cewa kawai dai baya bukatar ta ne cikin duniyarsa shiyasa itama ta ajjeshi gefe kamar yarda Baseera ta bata shawara akan ta ajje lamarinsa gefe in ba haka ba damuwa dashi da take yi sosai zai taba mata rayuwa ba kadan ba. A yanzu a daidai wannan lokacin komai take ji yana dawowa sabo fil! Ji take yi kamar yanzu komai ke faruwa ji take yi kamar yanzu ne suka hadu da Dr.Karami ji take yi kamar yanzu shakuwarsu ta wanzu a duniyar nan sosai take jin zuciyarta nayi mata tuni akan komai wani irin yanayi take jin jikin ta ya shiga komai take ji na canzawa numfashin ta take ji yana sauka a duk wata dakika da lamarin Dr.Karami sosai take jin bugun zuciyarta na sauyawa da duk wani lamarin Dr.Karami sosai take jin idanuwanta na bukatar ganinsa a daidai wannan lokacin sosai take jin zuciyarta da kwanyarta suna son tunaninsa. Runtse idanuwanta tayi da karfin gaske tana mai kai hannunta saitin da take zaton nan zuciyarta take ajje a kirji sosai take jin bugunta na sauya komai ma da komai ji take yi ya sauya a lokaci guda. Numfashi take ja a hankali har ta isa bakin katifarta ta baje tana mai duban saman dakin nasu zuciyarta sai zarya take yi da duk wani lamari da tunani na Dr.Karami lokaci guda taji wani murmshi ya subuce mata tuna rayuwarta tayi ita dashi a Asibiti... "wato sabo 'yar taki tayi kwantai ba mai so an gama yawan ta zubar shine yanzu take bibiyar samarin Hafsi ko to wallahi ba zata sabu ba bindiga a ruwa ko da bakar jaɓa take aiki ba ta isa ba tayi kadan mu zuba ni da ita shege ka fasa gata ga Hafsi nan ta cigaba da bibiyar samarin nata". Kamar daga sama Mariya taji saukar kalaman a firgice ta mike tayo waje Goggo Marka ta hango tsaye ita da Hafsat sai faman cika take yi tana bacewa duban Umma tayi dake zaune tayi banza da su kamar ba da ita take yi ba. Wani kallo Goggo Marka tayi mata kafun ta nuna ta da tsaya. "ke dan hular ubanki shine saurayin na Hafsi kike kokarin kwacewa saboda ke kin yi kwantar ko to wallahi baki isa ba tun wuri ki fita daga harkar Hafsi in kuma ba haka na rantse miki da Allah sai kin sha mamaki na". Fakare Mariya tayi mamaki ya cikata ga mari ga ansar jaka duk ba su isa ba ita batayi magana ba sai su ne za su zo suna gaya mata magana har sun manta waye Huzaif a wajanta har suke kokarin ci mata mutunci wani murmushi mai ciwo ya kufce mata ta dubi Hafsat da Goggo kafun da girgiza kai domin ita dai abin ta rasa ma gane kan sa wai kiri-kiri sai faman IHU BAYAN HARI suke yi gabadaya sun mance baya sun mance waye ita har da suke duban idanunta suna fadi mata haka ji tayi kamar ta buɗe baki ta mai da musu da martani amma ina ba zata iya ba domin sa tasan ran Umma in yayi dubu sai ya baci shirun shine mafi alheri a gareta da sauri ta juya ta koma cikin daki zuciyarta a cunkushe ji take yi kamar ta daura hannu akai ta kurma ihu don bakin ciki da takaici. "FASHIN SAURAYI?". Ta ambata cikin wani irin yanayi mai haifar mata da wani lamari mai girman gaske mamaki abin yake bata wani lokacin kuma ya bata bakin ciki da takaici bata ganin laifin kowa sai Huzaif tayi mamaki da canzawarsa tayi mamaki da lokaci guda soyayyar da yake nuna mata ta gani kashe ni ta sauya gabadaya kamar bai taba furta mata KALMAR SO ba a duniyar nan komai take gani kamar a Mafarki. Nisawa tayi tana tuno lokacin baya yarda ya haukace akanta yana nuna yana son ta amma yanzu kamar bashi ba ta ga laifin Hafsi ba domin sai bango ya tsage kadangare ke samun mafaka kuma tayi alkawari ita da Huzaif har abada zata nuna masa ta fi karfin wulakanci da cin zarafi za ta nuna masa ita mace ce mai daraja da kima wacce ta san kanta ba irin matan da suke ɓarin jiki bane wajan kai kawo wajan saurayi ta daina damuwa dashi ta daina damuwa da bakin cikin da suke tura mata shi da Hafsat. *_KAMALA MINNA_*😘😘😘 [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA TALATIN DA HUDU. A firgice ya farka daga barcin da yake yi mai dauke da wani RIKITACCEN AL'AMARI wanda ya kusan sanya zuciyarsa da kwanyarsa daina aiki na wucin gadi sosai ya firgita da mafarkin barcin da yake jin sa kamar a zahiran ce ne ya faru ba wai a badinance ba. Da sauri ya zuro santala santalar kafafuwansa da hutu ya gama yi musu ƙawa a hankali ya sanya takalmarsa da suke bakin gadon ajje masu matukar kyau da burgewa kallo daya zakayi musu ka gane na zallar fata ce. Mikewa yayi kan kafafuwansa jikinsa sanye da Boxer wanda ya kawo masa har gwuiwa sai singilet mai kalar ash-colour wanda tayi matukar kama jikinsa ta bayyanar da cikar halittarsa ta mazantaka yana da damatsa da budadden kirji sosai mai dauke da kwantaciyar suma mai santsi kugunsa kuwa ba shi da fadi sosai ya dan tsuke kadan. A hankali ya dauko jallabiyarsa mai ruwan jinin kare dake rataye ya sanyawa jikinsa wanda hakan ya kara haskakashi matuka Toilet ya nufa ya wanke baki sannan ya watsa ruwa sosai kafin ya fito ya shirya cikin Suit baka sosai ya gyara sajensa gami da tararren gashin kansa gyararre in ka gani sai ka rantse Shampoo ya saka masa amma ko kadan haka sufarsa take baka sidik sai sheki da take yi sosai ya ke kula da ita wajan gyara kwantattacen sajensa shima haka fuskarsa ta fito fes da ita manyan idanuwansa da dogon hanci gami da bakinsan dan madaidaici sun yi matukar tasira wajan kara ƙawata fuskar tashi. Cikin hanzari ya gama shirye shiryensa kafin ya dauke Berifcase dinsa da sauran karikitan sa ya fice daga cikin dakin ya kulle can harabar gidan ya nufa in da motarsa take park-space tun kafin ya isa gareta ya danna mata Remove ta saki wani dan sauti tare da dallo wasu kalolin haske masu kayatarwa isa yayi ya bude ya shige yayi mata key kafin ya danna Remove dan madaidai cin Get din gidan ya buɗe kansa da kansa ya cilla motar zuwa waje cikin yanayi na kwarewa a tuki yana ficewa Get din ya koma ya rufe kansa. Gida ne dan madaidai na zaman mutum daya kirar gidan da ka ganshi zaka gane gine akayi sa na burgewa kuma na zaman yan gayu. A hankali yake tuki yana jin yarda zuciyarsa da kwanyarsa suke kokari rakito masa lamarin da ya faru dashi a barcin sa da ya tashi a wayewar garin yau sosai ya ji zuciyarsa na kai kawo idanuwansa na buɗewa suna wanzar masa da komai kamar yanzu komai ke faruwa runtse idanuwansa yayi yana mai daura hannunsa daya saman goshinsa a hankali yake furta. "Yaa Allah what is wrong with me?". Numfashi ya ja ya fesar kafin ya ware idanuwansa jin da yayi ana ta danna masa Horn sosai ya zaro idanuwansa waje ganin in da yake yayi mamaki sosai bai yi zaton ma wai tuki yake yi ba ya dauka yayi Parking domin ji da yayi akan sa a wata duniyar cikin sauri ya taka burki yana mai ambaton sunayen Allah kafun ya hada kansa da sitiyarin yana mai da numfashi. "Yaa Allah wai shin me ke faruwa dani ne haka?". Ya tambayi kansa tambayar da ya san ba wai yana da ansar ta ba ne komai yake ji a yau ya canza masa komai na duniya yana juya masa wani iri daban ba yarda ya sa ba ji ba zuciyarsa yake ji tana kai komo da wani lamari mai girman gaske wanda yake kokarin hana shi kwanciyar hankali da natsuwa. Tafiya mai 'yar tsayi yayi kafun ya isa Asibitin *Fortis Escorts Heart Institute* dake birnin Delhi a nan India da yake aiki a harabar yayi parking kamar yarda sauran yan uwansa likitoci sukayi ya jima kafin ya fito daga cikin motar don kuwa jin zuciyarsa yake tana kara narkewa da wannan lamarin da bai yi zaton lamarin har ya kai har haka ba ya jima yana binnewa a zuciyarsa ya jima yana dakon lamarin yana boye duk wata hanya da zata taso masa dashi ta hanashi kwanciyar hankali sosai yake danne zuciyarsa sosai yake hakurkurta da zuciyarsa akan lamarin da yake zaton ba zai taba kasancewa ba ko da kuwa ba azahiri bane ya raina lamarin rainuwa mai girman gaske amma a yanzu a wannan ranar a daidai wannan lokacin komai na shirin canza masa komai na shirin juye masa komai na shirin birkice masa ba tare da zato da tsammani ba. A hankali yake takawa idanuwansa na bin sashi da sashi na cikin asibitin har ya isa babbar kofar da zata sa dashi da Reception din. Kallo daya zakayi wa asibtin ka gane babba ne sosai domin akalla benensa zai kai hawa biyar zuwa shida cikin asibitin kuwa ko ina malale yake da tayal mai matukar daukar idanu da burgewa yanayin tsarin ma'aikatan dake zirga-zirga da kai komo kawai in ka kalla zaka gane ba karami asibiti bane lura da yanayin sa na kudi ne (Privet Hospital). Haka Dr.Karami ya shiga taka kafafuwansa cikin asibitin ko wani bangare yabi sai ya daga masu hannu suma suna daga masa suna mai furta 'Morning' komai da yake cikin sauri yake yin sa saboda lura da yayi ya kusan makara sosai a haka har ya isa bangaren da Offices din sa yake da hanzari ya buɗe ya shiga yana mai yasar da Brifcase dinsa saman Table din tare da sauran hargitsen dake hannunsa danginsu waya da key. Rufe idanuwansa yayi yana mai jan numfashi kafun ya isa kan kujerarsa yana mai cire Coat din saman suit dinsa yana mai rataye ta jikin kujerar zama yayi sosai yana mai jujjuyawa hannayensa saman kan sa jinsa yake yi a wani mataki na musamman wanda tunda lamarin yake faru dashi bai taba yi masa tsamari kamar na yau ba sosai yake jin zuciyarsa na ansawa kwanyarsa na rikicewa da lamarin da ya dauka ba mai sauki bane gareshi sosai yaji a daidai wannan lokacin ya na bukata komawa gida sosai yake jin zuciyarsa ta shiga azalzalarsa da ya tashi ya tafi sosai kwanyarsa ke tunano masa kasar sa. Numfashi ya ja mai zafi yana fesar wa kafin ya mike tsaye cikin wani irin yanayi mai matukar razana zuciya da ruhi Table din dake gabansa ya kai wa bugu wanda sai da kayan da suke kai sukayi rawa sosai a hankali ya shiga safa da marwa cikin Office lokaci guda wani gumi yaji yana ke to masa wanda bai san ta ya ya hakan ya faru ba hannunsa ya dungule waje guda yana mai sakin wani numfashi mai zafi. Kofar da yaji an taɓa ne ta sanya shi saurin juyawa ya fuskance ta idanuwansa a lokacin sun fara canzawa suna lumshewa kamar me jin barci. "Dr.Vijay". Ya fadi can kasar makoshinsa cikin halin damuwa. Murmushi ya sakar masa yana mai karasowa inda yake tsaye hannu ya mika masa. "Kayi latti yau zuwa na kusan uku ban samun ka abin ya bani mamaki ban san ka da haka ba ban san ka da latti a wajan aiki ba domin kai sam baka African Time kamar mu Why?". Ya fadi yana mai sauke idanuwansa sosai akan na Dr.Karami da yayi masa kuri kamar mai son fahimtar wani abu game dashi kafin ya kau da idanuwansa yana mai jan numfashi mai zafin gaske wanda yake ji har zuciyarsa tururinsa na kai masa yana haifar masa da wani irin yanayi a ƙasar ruhinsa. Sosai Dr.Vijay ya lura da yanayin da yake ciki kamar akwai abin da ke damunsa bisa lakari da yayi da yarda idanuwansa da fuskarsa suka canza lokaci guda kamar ba nasa ba hannu ya kai ya dafa kafadarsa murya a tausashe. "Dr.Karami something is wrong with you I think?". Ya fadi yana mai kuresa da kallo. "I don No but Dr.Vijay...". Hannu ya daga masa kafun ya ja hannunsa su karasa wajan kujerun dake fuskartar juna guda biyu na tsakiyar Office din zaunar dashi yayi kafun shima ya zauna ya na mai dubansa sosai yanayin sa kawai yake karanta da yanayin Emotion din sa gami da Tension din sa da suka sauya sosai da sosai hannunsa ya kamo ya sarke a tsakanin nasa. "Me ke damun ka Dr.Karami?". Ya tambayeshi gami da kuresa da idanu. Girgiza kai ya shiga yi kafin lokaci daya ya mike yana kwace hannunsa. "I Need To Go Home Right Now". Ya fadi yana mai dafe kansa da wani irin numfashi da yake fesar wa mai zafin gaske gabadaya ya rikice lokaci guda zuciyarsa yake ji ta azalzalsa ji yake yi kamar zata tarwatse jin komai yake yi na jikinsa kamar zai narke kawai gida yake so ya koma kasar sa yake bukatar ya gansa a ciki baya so ya kara ko da kwana daya ne ba ma kwana daya ba ko awa daya baya bukatar ace ya kara jin sa yake yi kamar in ya cigaba da zama zuciyarsa zata buga a ko wani lokaci zuciyarsa ta gaji matukar gajiyawa. "What? Dr.Karami you need to go home? Akan wani dalili?!". Mikewa yayi kan kafafuwansa yana dubansa cikin wani irin yanayi na mamaki da tu'ajibi kafin ya shiga nuna sa da hannu. "Anya kalau kake kuwa da alamun akwai abin dake dawainiya da kai in ba haka ba ana cikin tsakiyar aiki rana daya kace zaka tafi Najeriya wannan ba zai taba yuwuwa ba Dr.Karami ka canza tunan...". "Dr Vijay!". Dr.Karami ya fadi muryarsa da sauti sosai idanuwansa izuwa lokacin sun kaɗa matuka duban sa yake yi cikin wani irin yanayi kafun ya narkar da muryar. "I Need Help Please ka taimaka min ina son naje gida a yau din nan ba zan iya cigaba da zama ba domin kuwa sosai da sosai nake ji a jikina kamar akwai abin da ke kokarin faruwa dani zuciya taba kaji...". Ya fadi yana mai kamo hannunsa yana kaiwa saitin kirjin nasa yana mai lumshe idanunsa. Ware idanu Dr.Vijay yayi sosai jin yarda bugun zuciyarsa yake sauri a ko wani lokaci yana kara sauri kamar wanda yayi matsananci gudu. "...ina so a yau din nan na bar Delhi Dr.Vijay ina so ka saman min jirgi da zai dauke ni ya fita dani daga wannan kasar cikin mintina". Yanayin da yake maganar a hargitse kamar wanda ya kamu da hauka ya sanya Dr.Vijay saurin rikesa yana mai bubbuga bayansa a hankali kafin ya fara magana cikin sanyin murya. "Cool Down mana aboki na fada min meya same ka mai yasa kake so ka bar wajan aikin ka a irin wannan lokacin da ake matukar bukatar ka ya kamata ka zauna kayi tunanin kafin ka zartar da hukunc...". "Dr.Vijay Please mana". Ya fadi yana mai katse shi cikin yanayi na bukata sosai da gajiya da maganar da yake yi masa. "Dr.Karami". Dr.Vijay ya fadi yana mai sakin sa yana mai duban idanuwansa. "...Kasan dai yau ba zaka samu jirgin ba ko duk jiragen dake tashi ba wanda zai yi wajan kasarka ko don haka ya zama dole kayi hakuri zuwa gobe...". "Ba zan iya ba Dr.Vijay ba zan iya sake ko da awa ba ne akasar nan kawai ka taimaka min ko babu jirgin da zai tashi yau to ni kaje kayi mani Boking na jirgin gabadaya zan iya daukarsa ko nawa ne kuwa zan biya". Ware idanu yayi sosai jin abin da Dr.Karami yake fadi kamar wanda bai da hankali. "What? Dr.Karami jirgin ne zaka dauka zuwa kasarku...Ina hakan ba zai taba yuwuwa ba kasan kuwa ko zaka samu nawa zaka kashe...". "Wannan ba damuwa ta bace kawai kayi mani abin da nace maka in zakayi". "Gaskiya da matsala ba zan iya ba domin ko nace zan iya nayi maka karya". "Shikenan Nagode". Dr.Karami ya fadi rai bace yana mai zubewa kan kujera cikin tsananin bacin rai hannayensa duka saman kansa da yake ji yana barazanar tarwatsewa zuciyarsa yake ji tana yi masa zafi da raɗaɗi ji yake yi kamar ya farka kirjinsa ya zaro ta ya ajje ta waje. Dr.Vijay da yayi fakare yana dubansa gabadaya yaji lokaci guda ya bashi tausayi duk da dai bai san abin da ya saka abokin nashi cikin wannan halin ba amma ya tabbata abin ba mai sauki bane sosai ya lura dashi ya fice daga hayyacin sa sosai. A hankali ya fara takawa har iyasa gareshi kafadarsa ya dafa yana mai bubbuga masa baya a hankali. "Kayi Hakuri don Allah duk da dai ban san abin da ke damunka ba amma na tabbata ba mai sauki bane amma kayi hakuri zuwa gobe please nayi maka alkawari jirgin farko da kai zai daga...". Hannu ya daga masa cikin wani irin yanayi. "Please ka rabu dani kawai tun da ba zaka yi mani abin da na bukata ba ni ma ai ba nakasasshe bane zan iya da kai na". Da hanzari ya mike yana faman huci har lokaci hannunsa na kansa key din motarsa ya dauka yana kokarin fita Dr.Vijay yayi saurin rikesa sosai runtse idanu Dr.Karami yayi kafun ya buɗe su da wani irin yanayi na bacin rai a cikin su. "Please sake mani hannu Dr.Vijay tun da nace kayi mani kace ba zaka yi ba ban ga dalilin da zai sanya ni kuma ka hanani yi ba wanda kuma bai zai taba yuwuwa bane". "Ban san ka da gardama ba, ban saba ganin ka cikin wannan halin ba, ban san ka da zafin zuciya har haka ba, Dr.Karami karka canza yanayin da nake kallon ka dashi na mutumin kirki mai hakuri da kai zuciya nesa karka canza kallon da nake maka a matsayin mai TAWAKKALI akan duk abin da ya same ka kaifa musulmi ne ya kamata ace kana rungumar ko wani irin yanayi ka samu kan ka aciki ya kamata ace kana danne zuciyarka akan duk abin da zata bijiro maka dashi wannan tashin hankalin da ka saka kan ka a ciki bana tunanin shine maganin abin da yake damun ka ya kamata ka sassauta ka mai da komai ba komai ba sannan kayi tunanin abin da ya dace duk abin da hakuri bai bayar ba bana tunanin rashin sa zai bayar". Juya yayi ya dube shi yana mai sakin ajiyar zuciya kafin ya ja jiki ya isa kan kujera ya zauna yana mai runtse idanuwansa gabadaya hakan da Dr.Vijaya ya gani ya tabbatar masa Dr.Karami ya fara saukowa don haka ya isa gareshi yana bashi baki da tausasa zuciya a hankali zuciayarsa ta fara rage zukin da take yi masa da rikicin da kwanyarsa take masa don ya tabbatar maganar Dr.Vijay gaskiya ne shi a karan kansa ya sani duk haukar da yake yi nacewa zai bar Delhi a yau ya san hakan ba yuwuwa zai yi ba domin kuwa ya san ba jirgin a yau sai dai zuwa gobe din. Sun jima Dr.Vijay na bashi baki kafin ya hakura zuwa goben amma yarda yake jin zuciyar tashi kamar ba zata iya barinsa ya kai goben ba duk da hakurin da ya jona mata. A ranar dai haka ya wuni ba tare da tabuka komai ba illa kai kawo da yake tayi a cikin Office din har zuwa lokacin tashin sa yayi a lokacin ma sai da Dr.Vijay ya sake dawowa ya din ga bashi baki har gida ya rakashe ya tabbatar da ya hakuri din sannan ya barshi sukayi sallama. Ko da dare yayi kasa barci yayi domin gani yake yi kamar in ya kwanta din zai makara ko da dai Dr.Vijay yace zai yi masa komai kafin gobe din har da su Viza duk zai samar masa amma duk da hakan hankalin sa bai kwanta ba haka ya dinga safa da marwa da ya kwanta sai ya tashi yashiga zarya a daki daga daki zuwa falo lokaci-lokaci yana duban Agogo sam! ya kasa tsayawa waje daya kamar wanda yake fama da basir zaman ma ya gagareshi a tsaye ya dinga gangaɗi da yaji yana kokarin fin karfin sa sai yayi Toilet ya wanko fuskarsa ya dawo haka ya dinga yi har zuwa lokacin da barci barawo gwanin iya sata yayi awan gaba dashi bayan ya zauna a kan hannun kujera bai san lokacin da ya tuntsure a cikinta ba. Misalin karfe hudu ya farka a firgice kamar wanda aka shekawa ruwa da sauri ya dubi Agogon falon ganin karfe hudu da yan mintina ya sanya shi ware idanu ya na mikewa cikin hanzari yayi hanyar Toilet da gudu kamar wanda gudawa take kokarin kufce masa bai dau tsawon wani lokaci ba ya fito ya shirya cikin kananun kaya da sukayi matukar amsarsa ya gyara sumar kansa da sajen fuskarsa, fuskarsa tasa tayi fayau sai idanuwansa da suka dan kumbura na rashin isasshen barci da bai yi ba karamar jaka ya dauka ya zuba abin da yake bukata na tarkacen sa kaya ko kala daya bai dauka ba bayan na jikin sa. Wayarsa ya dauka ya danna wa Dr.Vijay kira a daidai lokaci agogo ya buga karfe biyar minti kamar uku aka dauka kafin ya dau wayar don har ya fara rawar jiki jin an ansa shi ya sanshi saurin yin magana baki na rawa. "Morning Dr.Vijay ni fa na gama shirina ga ni nan zuwa...". Zabura Dr.Vijay yayi daga kwancen da yake idanuwa a warwaje. "Ka shirya kace? kai kam kalau kake karfe nawa yanzu ka sani? don Allah Malam ka koma ka kwanta don nasan da alamun ko barci bakayi ba jirgin fa ma sai biyun rana zai tashi". Wata ashariya Dr.Karami ya dauko ya sauke. Sai da Dr.Vijay ya tsorata duk da dai bai san abin da yace ba amma ya tabbatar abun ba mai kyau bane. Cikin bacin rai Dr.Karami ya dora da cewa. "Ban son wulakanci kaji ko ta ya ya zaka ka ma min jirgin rana nida nake so na tashi da safiyar nan ban so rana ta fito ta tadda ni a kasar nan". Dariya sosai Dr.Vijay yayi kafin yace. "Wai anya ba Amarya aka ce an baka ba kake wannan rawar jikin ni abin naka ne naga ba sauki...". "Ka ga don Allah Malam karka bata min rai kuma ka taso kawai ka zo ka dauke ni ko kuma na fito yanzu ka ganni a gidan ka". "Allah ya baka hakuri bani 30Mins yanzu zaka ganni". Sauke wayar yayi yana faman tsuki jakarsa ya dauka ya fito falo duk ya kashe kayan wuta da suke jone kafin ya fito ya kulle kofar fallon sannan ya yi wa motarsa securty-Key ya samu waje ya zauna a harabar gidan yarda kasan wanda aka koro sosai ya ƙagu duk bayan mintina biyu sai ya dannawa Dr.Vijay kira tun yana dauka har ya daina hakan ya kara tunzura Dr.Karami daga karshe ma da yakira Dr.Vijay sai yaji wayar akashe hakan yayi matukar kular dashi da hanzari ya mike yana kokarin buɗe motarsa yaji Horn wata irin ajiyar zuciya ya saki kafin ya figi jakarsa yayi waje cikin hanzari Dr.Vijay ya hango yayi parking yana kokarin fitowa daga cikin motar sai da galla masa harara kafin ya jingina da motar ya harɗe hannayensa a kirji yana faman dubansa fuskarsa a tsuke a haka Dr.Karami ya kulle gidan ya karaso wajansa. "Wai ma na tambayeka duk wannan ɓarin jikin da kake yi ka nemi izini daga wajan aiki ne jiya". Wani irin duba yayi masa kafin ya isa ya buɗe motar ya cillar jakarsa ciki ya juyo ya dube shi. "Ban yi ba kai yau sai kayi mani ko?". Ya fadi yana faman murmushin yake. "Ai wallahi baka isa ba in ka ga na rakaka Airport to wallahi muje ka nemi izini ne". "Yaa Allah wai shin me yasa kake son takura mani ne har haka mai yasa kake son bata min rai ne?". "Ni ban bata maka rai nayi ba gaskiya ce na fada maka". "Ni gaskiya at this Time ba zan iya zuwa ba sai dai ka taimaka in kaje ka nema min". Gyaɗa kai yayi kafun ya juya ya shige cikin motarta kafun shima Dr.Karami ya shige yana faman lallashin Dr.Vijay akan ya taimaka in yaje Asibiti ya neman masa izini gami da tafiyar da zai yi shi dai Dr.Vijay bai ce masa komai ba haka ya figi motar suka dauki hanya domin zuwa Airport. Cikin mintina da ba su haura ashirin ba suka isa Airport jirgin karfe bakwai Dr.Karami zai hau domin keta hazo zuwa kasar sa Najeriya. Dr.Vija sai iya shege yake masa wai bai yarda dashi ba anya rawar jikin da yake yi ba amarya aka bashi ba ya matsu yaje ya kanta. Shi dai yaƙe kawai yake yi masa domin dai a daidai wannan lokaci. ya matsu ya ga jirkin su ya tashi ya sauka a kasarsa. Bakwai da minti biyar jirginsu Dr.Karami ya daga zuwa najeriya. ******** Ya mutsa fuska tayi tana mikewa kan kafafuwanta duk ta hada gumi a goshi hannunta face-face da kwabin fulawar Cake duban Umma tayi kamar za tayi kuka domin kuwa gabadaya take jin jikinta yayi sanyi da nauyi kamar wacce aka doddokewa kafadu lokaci-lokaci tana jin gabanta na faduwa wanda ta rasa dalilin haka tun da garin Allah ya waye a yau take jin ta a haka kwabin Cake din sai dakyar take yin sa jin Umma tace bazata yi mata ba ta gaji da son jikin da take yi sai kace mai laulayi. "Don Allah Umma ki karasa min wallahi ba dadi nake ji ba a jikina". Wani kallo ta watsa mata kafun ta dubi kwabin Cake din. "Ai ke zan ga ranar da zaki daina son jikin nan naki wallahi kina mace amma ke gabadaya kamar wata mage ai ko mage ba zata nuna miki son jiki ba yarda ki kasan ruwa haka kike kuma ki karasa kwabin ki don ba yi maki zan yi ba ga dai yamma dai nan ta sako kai in kika bari har aka kira magrib wallahi ba zan tayaki aikin daren nan naki ba barci na zanyi". Marere ce fuska tayi kamar zata fashe da kuka. "Haba don Allah Umma daure ki karasa min...". "Yaa Allah wai Mariya na tambayeki haka in kika yi aure zaki je kina wa mijin ki wannan SANGARTAR aiko tun wuri ki sauya don ba a san mace da nawa ba duk mace mai nawa sai kin same da kazanta da rashin sanin yarda zata kula da gidan auren ta". "Naji Umma don Allah tausaya min Allah bana jin dadin jikina ne gabadaya yau din nan...". "Sannu. ba rashin jin dadi ba kece General Hospital karewarta". Umma ta fadi tana kokarin mikewa a daidai lokacin Mu'azzam yashigo da gudu ba in da ya dosa sai wajan kwabin Cake din ganin haka da Mariya ta yi ya sanyata saurin hanzarin cafko shi tana matse masa kunne. "Sannu Biri sarkin barna wai kai don Allah Mu'azzam baka gani dai ka kyale sai ka bata ko to wallahi zan dinga dukan ka bar ganin Umma na goyan maka baya". Turo baki yayi gaba kamar zai fashe da kuka Umma da ke tsaye ta shiga yi musu dariya. "Yo cewa fa kikayi kin gaji ba sai ki barshi ya karasa miki ba ai sha yanzu magani yanzu ne Auta ba shi da jinkiri in dai wajan aiki ne yanzun nan zai yi sa yaro ba kiwa kenan". Ware idanu Mariya tayi gami da tura baki gaba kamar zata rushe da kuka ta dubi Mu'azzam da yake kici-kicin kwace kansa ta tallake masa keya. "Kai Umma wannan yaron naki ke kike goya masa baya kullum in zan yi kwabi sai ya nemi bata min bayan kuma in nayi duk shi yake cinye 'yar ribar". "Kan ki ake ji miko min kwabin na karasa miki don na lura in na biye miki wannan kwabin sai ya dauko lalacewa". Ai sai ta saki dariya da hanzari ta saki Mu'azzam ta dauki kwabin ta mikawa Umma da sauri ta shiga wake hannayenta cikin kwanon dake girke da ruwa a ciki. Doguwar rikace a jikinta sai kallabi da ta daura kan ta dashi fuskarta fayau ba alamun kwalliya amma hakan bai hana sirrin kyanta fitowa sosai da sosai doguwar rigar ta anshe ta ta dan kamata kadan daga kugunta wanda yake cike sosai daga cikinta kuwa a matse yake kamar wacce bata cin abinci kirjinta ya cika sosai har yana kokarin rinjayarta saboda rashin ƙiɓarta doguwa ce amma ba can sosai ba jikinta kiran coca-cola ne. A hankali ta warware dan kwalin kanta bayan ta matse daga kusa da Umma tufkanken gashin kanta ya baje sosai wanda yake ta faman sheki da daukar idanu a hankali ta shiga tattare shi a daidai lokacin wani kamshi mai dadin shaka ta ji ya doki hancinta da sauri ta ware idanu gami da kara buɗe hancin nata don sosai kamshin ya tafi da imaninta a daidai lokacin kuma wata murya wacce ta kusan narkar da Mariya kasa tayi Sallama wanda ya sanya gaban Mariya dokawa cikin wani irin yanayi mai razanarwa sumar tsaye tayi a daidai lokacin da ta daga fararen idanuwanta manya ta sauke su akan saitin mutumin dake tsaye cak! A kofar fuskarsa da wani irin yanayi idanuwansa dauke da wani kallon da ya sanya numfashinta kusan daukewa.... *_KAMALA MINNA_*😘😘😘 [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA TALATIN DA BIYAR. Numfashin ta take ji yana fizga kamar zai bar jikinta wani irin juwa da jiri taji tana kwasarta kamar zata watsar da ita kasa idanuwanta sun ya cak! waje ko juyawa ba sayi sosai take dubansa da kallo na mamaki da wani irin yanayi zuciyarta take ji tana bugawa da duk wani jan numfashin ta kamshin take ji yana dokar mata hancinta wani irin yanayi wanda ya haifarwa jikinta da wani irin kasalallan yanayi jikinta take ji yana narkewa kamar ruwa kafafuwanta sai ƙarƙarwa suke yi suna kokarin zubda ita kasa. Juyar da take ji tana wani irin juyawa da ita kamar wacce take samar gajimare runtse idanuwanta tayi a daidai lokacin da ta hango wasu abubuwa sun fito daga idanuwansa sun dire ana kamar saukar KIBIYAR AJALI lokaci guda zuciyata ta buga da wani irin yanayi mai girman gaske. Sosai taji zuciyarta na buɗe a wani killataccen waje wanda ya jima kargame da katon kwado makullin sa ita kanta ba ta san inda ta jefashi ba sosai ta ji zuciyarta ta sauya bugu da wani al'amari mai girman gaske. Ganin komai take yi tamkar a mafarki ba a zahiri ba ganin komai ta ke yi kamar ba a duniyar zahiri yake faruwa ba magudanan jinin jikinta take ji sun sauya a wani mataki wanda ita kanta ba zata ce gashi ba kwanyarta ta shiga kai kawo da wasu lamari masu yawan gaske wanda ta jima da binne su a zuciyarta. A hankali take buɗe idanuwanta hancinta na sake dauko mata daddar kamshin sa wanda yayi matukar tasiri wajan juyar mata da duk wani kamshi da ta taba ji a filin duniyar nan. Da sauri ta shiga warware dan-kwalin da ke kanta jikinta sai kyarma yake yi idanuwanta akansa har yanzu zuciyarta ba ta gama yarda da cewa shi ne ba sosai take ganin komai tamkar a mafarki dan yatsanta guda ta daga tana mai nuna shi bakinta na wani irin ɓari kamar wacce ruwan sama yayi wa dan banzan duka take rawar sanyi. Shikam! mutuwar tsaye yayi zuciyarsa na bugawa da wani irin yanayi sosai yake yajin sa a sama duniyar na kai kawo dashi komai yake ji na kwanyarsa na wargajewa zuciyarsa na buɗe wani makeken fili tana dasa wata bishiya mai girman gaske wacce tayi rassa a lokaci guda duk ta mamaye kafatanin filin zuciyarsa. Murmushi yake saki wanda shi akaran kasa bai san yanayi ba idanuwansa na juyawa da wani lamari mai girman gaske sosai idanuwansa suke bin Mariya da kallo kafun ya kau da kai cikin yanayin na bugun zuciyarsa da yake ji kamar zata tarwatse. A hankali yashiga kokarin saita kansa yana jan numfashi mai taurin gaske kirjinsa yake ji yana nauyi sosai da wani abu mai girma gaske a hankali ya runtse idanuwansa. "Yah Dr.Karami". Mariya ta furta da wani irin sauti a muryarta wacce bata sam ma tana dashi ba bata san ta yi amfani dashi ba sosai take kallonsa sosai take jin jikinta na ansa wasu sakonni masu narkar mata da zuciya su hargitsa mata tunani. Murmushi yayi kafun wani abu da ya tsaya masa azuciya ya wuce bayan ya haɗeshi dakyar. Sautin muryarta da yaji yana ansa kuwwa a kunnuwansa hakan ba karamin narkar masa da jiki yayi ba gabadaya ji yayi sautin yana bin jikinsa yana ansa kuwwa a kwanyarsa da wani irin yanayi mai girman gaske. "Mariya". Ya fadi zuciyarsa na wani irin zillo kamar zata faso kirji ta yo waje. "Yaa Allah Mariya wai da gaske kece?". Ya sake fadi da wani murmushi mai kama da son fashewa da kuka idanuwansa naa kara narkewa da wani irin ruwa kamar na Rose tsakiyar kwayar idanunsa wani haske mai kama da na kibiya yake fitowa da sauri-sauri yana isa ga Mariya da ta gama narkewa cikin wani hali zuciyarta na wanzar da wani farinciki mara musaltuwa ji take yi kamar ta daka tsalle ta isa wajansa ta rungumeshu duniyar take ji tana sauyawa da duk wani hali da take ciki duniyar take ji tana kamfato mata wani farinciki tana ajje mata runtse idanu tayi jin abin da yace da sauri ta juya wajan da su Umma suke wayam! ta ga wajan ba kowa wata ajiyar zuciya tayi kafin taja kafa cikin sauri ko wani sashi na jikinta sai kaɗawa yake yi musamman kugunta da kirjinta. kafafuwanta kawai zaka kalla ka gane a harɗe suke tafiyar take yi amma ji take yi kamar zata kifa. Fakare yayi da baki fuskarsa da wani kayataccen murmushi mai girman gaske idanuwansa kawai yake yawatawa akanta mamaki ne da tu'ajibi suka cika shi har yanzu zuciyarsa bata gasgata masa wai Mariya bace gani yake yi kamar wata halittace daban a tsaye a gabansa take yi masa magana gani yake yi kamar wata daban ce take tafiya a yanzu ba Mariya da yasani shekaru hudu baya ba komai ya sauya komai nata ya canza muryarta kirar jiki ta yanayin tafiyarta... "Yaa Allah". Ya furta yana kai hannayensa yana muttsuka idanuwansa da yake zaton karya suke yi masa gizo suke yi masa da wata mace ba Mariya ba zuciyarta na kara gasgatawa amma shi yaki AMANNA dan yatsarsa daya ya saka cikin baki yana cizawa da karfi jin zafin ya sanya shi sakin kara mai dan sauti. "Ouchhh!!". Ya furta yana yarfar dan yatsar nashi. Ko da Mariya ta shiga dakin Umma na zaune tana karasa kwabin Cake din bango ta jingina dashi tana mai da numfashi da sauri-sauri idanuwanta a lumshe fuskarsa nayi mata yawo a idanuwanta murmushisa idanuwansa kai gabadaya ma fuskarsa take ganin tana kai kawo a cikin runtsantsun idanuwanta zuciyarta na wata irin harbawa da wani irin yanayi mai girman gaske numfashi ta ja kafun ta buɗe idanuwanta a saitin Umma da tayi mata fakare tana kallon Ikon Allah wai akace in kana da sauran numfashi kana DA SAURAN KALLO a filin duniyar nan mamaki ne ya cikata lokaci guda da taga canzawar Mariya yanayi da take kallon fuskarta da yanayin da jikin nata ya nuna wanda a tsayon lokaci mai yawa bata ga haka ba ta mance rabon da ta ga Mariya a haka bazama ta iya tunawa ba. "Ke wai lafiyarki kuwa?". Umma ta fadi tana mai tsuke fuska cike da mamakin Mariya tun lokacin da ta lura da shigowar Dr.Karami da yanayin da ta ga Mariya a ciki shiyasa ta zare jiki ta yo cikin dakin don ta lura tsaf! Mariya zata yi abin da zai tasa ta ji kunya a gabansa bata iya ƙewar mutum ba sam! A duk lokacin da ta ga wani wanda suka jima ba su hadu ba ta dinga ɓarin jiki kenan amma na yau ya bambanta da sauran lokuta. Wani murmushi mai kwari ne ya kufcewa Mariya kafun ta kai hannayenta tana toshe bakinta har zuwa lokacin jikinta bai daina ɓari ba. "Yah Dr.Karami ne fa". Uwar harara ta watsa mata kafin ta ja tsaki. "Eh na san shine ai shiyasa na ga sai ɓarin jiki kike kamar wata sakarya ke a tunanin ki hakan da kikayi burgewa ce kina 'ya mace ki barin jiki ai sai ya dauke ki ba ki da natsuwa duk na ga abin da ya faru wanda sam bai dace ace ke a karan kan ki kike haka ba". Zaro idanu waje tayi jin abin da Umma ta fadi da sauri ta sauya fuska alamun damuwa zame jiki tayi ta zauna kasa don jin kafafuwanta take yi kamar ba za su dauke ba. "Au! zama kikayi ki bar shi a tsaye a tsakar gidan so kike yi ya lura da wautarki". Runtse idanu tayi zuciyarta na wata irin harɓawa da sauri ta mike tana kokarin ficewa amma ta kasa sai kai kawo take yi tana susar kai Umma na lura da yanayin ta da sauri ta mike ta shiga kintsa dakin duk da ba wata gyara yake bukata ba komai tsaf yake hijab dinta ta dauko ta saka kafin ta dubi Mu'azzam da yake ta kasumar Cake sannan ta dubi Mariya. "Ki dai kintsa ko". Ta fadi fuskarta a daure kasa Mariya tayi da kai kafun ta gyara daurin dan kwallinta ta dauko hijab ta saka ita ma gabanta har lokacin bai daina bugawa ba fargaba kawai take yi ji takeyi kamar in ta fita ba zata ganshi ba gani take yi kamar a mafarki ne. Numfashi ta ja kafun ta runtse idanu ta buɗe addu'a tayi domin samun sauki a zuciyarta. A hankali taka ta fice daga cikin dakin kanta a kasa har yanzu yana nan tsaye harɗe da hannayesa a kirji dago kanta tayi ta dubesa idanuwansu suka sarƙewa waje daya lokaci guda zuciyoyinsu suka buga a tare da sauri tayi kasa da kai ganin wani murmushi da ya saki da ya kusan tafiya da imaninta. "Sannu da zuwa Umma tace ka shigo daga ciki". Ta fadi a wahale kafun ta juya tana kokarin komawa dakin. "Bana son gaisuwar ai ni ba wajanki na zo ba". Dr.Karami ya fadi da rashin wasa a muryarsa cak! ta tsaya da tafiyar da takeyi zuciyarta tayi mata wani wawan bugu ta runtse idanu kafun ta juyo cikin tsuke fuska da gayyato juriya ta ajjewa kanta zuciyarta na tuno mata da abin da ya faru na halin ko in kula da ya nuna a kanta tsayin shekaru sosai zuciyarta ta fara dauko laifinsa duk da dai bai taka kara ya karaya ba. "Nima ai ba don halin ka na yi ba". Ta fadi tana mai hanzarin barin wajan ta fada cikin dakin. Murmushi yake saki yana mai nuna ta da hannu mamaki kamar ya kashe shi wai Mariya ce take magana haka ita ce tayi baki haka Mariyar da ya sani acan baya mai shiru-shiru magana ma wuya take yi mata wai ita ce da mai da masa da magana da yanayin fushi take yi dashi sai da ya gama shan sharafin mamakinsa sannan ya taka zuwa dakin a daidai lokacin ita kuma Mariya ta fito hannunta dauke da Jug na roba saura kadan suyi gware da sauri ta kauce ko kallonsa ba tayi ba fuskarta ba yabo ba fallasa yana kokarin mataa magana tayi masa wani kallo da ya sanyashi sauri sakin murmushi yana mai shigea dakin bakin sa dauke da sallama. Bayansa tabi da kallo kafin ta ajje Jug din tayi hanyar waje kankara ta sayo ta zo ta hada masa lemo mai kayan kamshi da yake Umma na ajje kayan kamshi da kayan jinja saboda irin wannan yanayi na bako idon kunya sosai ta hada lemon sai kamshi yake yi sannan ta farfasa kankara ta saka a ciki sai da ta bashi kamar minti daya sannan ta dauka domin kai masa fuskarta a gimtse sai ka rantse bata taba yin dariya ba murya can kasar makoshi tayi sallama ta shiga idanuwansa kuwa na saitin kofar tana shiga da idanuwansa ta fara cin karo da sauri ta dauke kanta ta isa garesa ta ajje a gabansa ta mike wani plat ta dauko ta zubo masa Cake ta zo ta ajje masa duk kanta na kasa ta ki kallonsa amma shi duk motsinta na idonsa hanyar waje tayi tana kokarin fita. "Mariya!". Umma ta kira da wani sauti na tuhuma da sauri ta juyo ta dubeta alamu tayi mata da ido aiko sai ta kara tsuke fuska tana turo baki gaba ta gefen ido ta kalli Dr.Karami ya dauki Jug din lemon yana sha amma idanuwansa na kanta da sauri ta fice daga cikin dakin. ****** Duban Baseera tayi a dan hargitse idanuwanta ta bude su sosai kafun ta watsa mata wani kallo. "Ke fa tsiyata dake wauta yasin daga fada miki magana kina kokarin canza mani manufa ta daban...". Wayar dake hannun Baseera ta daura Ringing da sauri ta duba lokaci guda ta balle da dariya tana duban Mariya da tayi fakare da idanuwanta kallo daya zakayi mata ka gane ba cikin hayyacin take ba. "Ke My Besty Mutumin ne fa yasin...". Duka ta kai mata kafun ta mike tana kokarin ficewa a daidai lokacin ita kuma Baseera ta daga tana ansawa ganin Baseera na kokarin fita tayi sauri dauke wayar daga kunnanta. "Billahillazi yana kofar gida ya biyo ki". a firgice Mariya ta juya tana dubanta Baseera dake faman kwasar dariya idanuwanta a warwaje lokaci guda suka kaɗa kamar za tayi kuka. "Yo ni mai ya dame shi dashi ai ba waje na ya zo ba...". Da sauri Baseera ta mike tana katse wayar da dariya a bakinta. "Yasin Karya kike daga gidan Umma yake yana nemanki Umma ta fada masa kika na nan yarinya kin gudu baki tsira bane bari ki ga". Baseera ta mike tana zarar mayafinta tana kokarin fita waje ganin haka ya sanya Mariya saurin riketa. "Ke fa ba hankali kika cika b ina kuma zaki kin san Allah ko kin je kin ce ina gidan ba zan fita ba domin kuwa ba abin da zan masa". Tagumi Baseera tayi da hannu daya kafun ta saki wata dariya. "Uhmm wai ma ni wallahi dariya kike bani mutumin nan yau satin sa kusan biyu yana zarya akan ki yana baki hakuri akan abin da yayi miki amma ke kamar wata dutse gabadaya kin kasa bashi lokacinki Mariya karki mance fa waye Dr.Karami karki mance lokacin da kika saka ni gaba akan baya kula ki ya manta dake amma yanzu dama ta samu kina kokarin sakinta". Haushi ne ya turnuke Mariya tayi sauri ta fizge jikinta daga Baseera ta koma bakin gado ta zauna ta na mai zabga tagumi fuskar nan a haɗe kamar hadari da sauri Baseera ta iso gareta tana mai dafa mata kafada. "Yi hakuri mutuniyar tashi don Allah muje bai da ace mutum kamar Dr.Karami kina yi masa haka ba...". "Don Allah ki rabu dani Baseera karki saka raina ya bace kisan Allah ba zan fita ba ai in na fita kamar bani da zuciya ne". Zaro idanu tayi waje kafun ta shiga dubanta sosai ganimn take yi kamar ba Mariya ba komai take ganin ya canza game da ita fushin da ba nata ba take ganin Mariya ta aro ta daurawa kanta akan mutumin da sam bai dace ace tayi wa haka abin yayi matukar daure mata kai don haka sai ta koma gefe tana mai latsa wayarta ta ba banza ajiyar Mariya. ****** Da sauri ta sauka a Napep din ta nufi hanyar shiga gida ko gabanta bata kallo idanuwanta gabadaya a rufe suke ba zato ba tsammani taji tayi karo da mutum da sauri ta dago kanta ta na fiddo su waje cikin yanayi na tsoro da firgita tsuke fuska tayi ganin wanda yake gabanta da sauri ta kau ce tana kokarin wucewa cikin gida caraf! taji ya rike mata hannu ai ji tayi kamar ta kurma ihu wani kallo ta watsa masa kafun ta fizge hannun nata rai bace ta shiga nuna sa da yatsa. "Huzaif kana da hankali kuwa kasan abin da kake aikatawa hannu na fa kari ke...". Wani kallo da yayi mata yana kokarin sake riketa da sauri ta ja baya kafun ta daga hannu ta zabga masa mari cikin tsananin takaici da bakin ciki. "An gaya maka ni irin watsantsun matan da kasani ne an gayamaka RA'AYINMU DAYA da su ne ko an gaya maka halayarmu daya da su ne tun wuri ka dawo hayyacin ka in kuma ba haka ba na rantse da Allah zan yi maka abin da baka taba zato ba". Murmushi ya saki yana yawatawa da idanuwansa a jikinta kafun ya shiga kokarin kaiwa gareta a hankali ta shiga ja daya baya idanuwanta a warwaje cikin tsananin tsoro da firgita yanayin da ta ga Huzaif a ciki ya tabbata mata ba ya cikin hankalinsa da sauri ta juya tana kokarin kwasa da guda sautin karar marin da taji ya karaɗe kunnuwanta ne ya sanyata tsayawa cak! kafin ta juya a firgice. "Dr.Karami!". Ta fadi a firgice jikinta har rawa yake yi wani irin huci yake yi kamar kumurci yana faman cika fuskarsa ta rine tayi jajir idanuwansa sun kaɗa sosai hannusa akan Huzaif da ya dafe kuncin sa domin kuwa sosai yaji shigar marin da Dr.Karami yayi masa kallon kallo suka shiga yi wa juna a tsakanin su sosai suka so tuna in da suka san junansu. Dr.Karami ya ja numfashi mai zafi kafun ya dubi Mariya da tayi matukar shiga firgice kamar wacce zata saki fitsari ba abin da jikinta yake yi sai rawa sosai ta tsorata da yanayin da taga Dr.Karami a ciki musamman irin kallon da taga yana watsa mata kau da kai tayi tana kokarin barin wajan wata irin razananniyar tsawa ya doka mata lokaci guda ta tsaya da tserewar da take kokarin yi a hankali ya shiga takowa inda yake gabanta na dokawa da tashin hankali mai girman gaske nuna ta yayi da yatsa bakin sa sai motsi yake yi yana son yin magana amma ya kasa ya dunkule hannu ya naushi iska yana mai cizon laɓɓansa kafin ya juya ya kalli Huzaif da har lokacin yake tsaye dafe da kuncin sa karasawa yayi gareshi yana kallonsa ido cikin idon kafin ya ja huci mai zafi. "In har kasa sake gangancin ka ya sake dibarka har kayi kokarin taba ko da gyalan jikinta ne na rantse maka da Allah sai na daureka har igiya tayi rara don na lura kuruciya na damun kwanyarka zan saita maka ita". A hansale Huzaif ya dube shi. "kan wannan kucakar yarinya ka mare ni kan wannan mai kama da birin ka mare...". Ji kake kau! Dr.Karami ya sake dauke shi da mari wanda yafi na dazu ya cakumi wuyar rigarsa. "wai kan dan gidan uban wanene fada min uban waye uban ka a garin nan na rantse da Allah in bakayi wasa ba kafatanin zuri'arku sai sun ji a jikinsu". Yana gama fadin haka ya watsar dashi gefe kafun ya dubi in da Mariya take cikin tsananin firgice da razana bata yi zaton zafin Dr.Karami ya kai har haka ba sosai taji tsoronsa ya sami ma sauki a zuciyarta kasa tayi da kai ganin wani kallo da ya watsa mata mai cike da tuhuma zuciyarta taji tayi wani irin dokawa da hanzari ya isa can gefen hanya in da yayi parking lokacin da ya ga abin da ke faruwa tsakanin Mariya da Huzaif a hanzarce ya isa yayi mata ki ya fizge ta cikin tsananin bacin rai huci kawai yake yi zuciyarsa na wani irin zafi da raɗaɗi ji yake kamar ya hada Huzaif din da Mariya yayi musa dan banzan duka. Sai da taga bacewarsa sannan ta juya ta dubi Huzaifa tana mai galla masa harara tayi hanyar shiga cikin gida a soro ta ci karo da Hafsat tana kokarin fitowa taci uban kwalliya da dinkin atamfa wanda yayi matukar kama mata jiki ainun in ka ganta sai ka rantse wata rikakkiyar wayayyice nan kuwa kanta empty ne a hankali take taku Mariya na binta da kallon mamaki da tu'aji bi da yarda Hafsat ta bari duniya ta buɗe mata ido haka ko da yake bata ga laifin ta ba Goggo Marka ce ta daure mata kugun yin abin da take so tun da suka hadu da Huzaif shikenan ta daina zaman gida kullum yana hanyar daukar ta suna ficewa ita dai nata ido domin bazata taba mance cin amanar da Huzaif da ita kanta Hafsat din sukayi mata ba kallon su kawai take yi girgiza kai tayi tana mai shigewa cikin gida zuciyarta a jagule komai take jin ya kwance mata duniyar gabadaya tayi mata zafi ji take yi kamar ba ita ba. "Kan Uban can!". Hafsat ta fadi lokacin da taga Huzaif na faman huci hannunsa dafe da kuncin sa idanuwansa sun kaɗa sun yi jajir kamar wanda kayi wa sura ce da barkono. "Me ya same ka haka?". Ta fadi tana mai duban sa, tsaki ya ja kafun ya shiga safa da marwa a wajan sai fama huci yake yi. "wani dan iska ne wai don kawai waccan yarinyar ta gidan ku za ta gaya min ba dadi shine ya zo ya daura min tafi a fuska". Zaro ido tayi waje kafun ta dubi kofar gidan su. "Mariya ko?". "to akwai wata yarinya ce a gidan ku bayan ita". Ya fadi a hassale kamar zai kifeta da mari ita ma tsaki ta ja tana mai galla masa harara. "Huzaif na lura so kake yi ka raina min hankali in ba don haka ba ina ruwanka da ita ai ko me akayi maka kai ka ja yasin". Wani wawan cafka ya kai wa hannunta ya murɗe ta saki kara mai sautin. "Ni zaki raina wa hankali Hafsat kin san Allah in bakiyi wasa ba sai na sauke akan ki". "Sauke mana in ka isa ai bani na saka ka kula ta ba Malam balle ka sauke fushin ka akai na". Dunkule hannu yayi kamar zai kai mata naushi amma sai ya bugi iska gami da jan tsaki ya isa in da yayi parking ya buɗe mota ya shiga ransa a bace zuciyarsa sai faman tururi take da takaici Hafsat dake tsaye ganin yarda ya shiga motar rai bace ba tare da yayi mata magana ba haushi ya cika ta ja tsaki kafin ta isa gareshi kallonsa kawai tayi ta watsar kafun ta buɗe motar ta shiga ko kula ta bai yi ba ya yiwa motar Key ya fizge ta ya bar layin yana mai fadin. "Billahillazi sai na baiwa Mariya mamaki ba dai ni ta saka akayi wa cin mutuncin ba zan nuna mata na fita iya shege". Hafsat da ta kula tsaki taja a ranta tana fadin 'Allah ya kara ai ni nafin son haka dama kiyayya mai karfi ta ratsa tsakaninku'... *_KAMALA MINNA_*😘😘😘 [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA TALATIN DA BAKWAI. A hankali take taka benan har ta isa bakin kofar tana jin yarda gabanta ke dokawa ba ta san ya zai kalleta ba bata san ya zai karbeta ba ita dai ta san tana son sa so mai tsanani wanda tun da take a filin duniyarta bata taba jin son wani ɗa namiji ba kamar Dr.Erena zuciyarta da ruhinta sun jima suna kai kawo akan son shi ta dalilin son sa ta zo aiki cikin Company sa saboda burinta ya cika take zaman aiki a company ba wai saboda kudi ba amma ta rasa ya zatayi ta rasa mai ya dace tayi a gareshi domin ya amince da ita har ya so ta sosai ta lura sam! baya kula duk yanayin da take nunawa don ya sota amma hakan sam ba ya wani tasiri akansa ba ta san ya za tayi ba abin da ya ke kara tayar mata da hankali yarda lokaci guda wata ta shigo cikin Company din take kokarin bata mata duk wani shirinta ta lura Dr.Erena son ta yake yi so kuwa mai tsanani abin da ta lura dashi ita Areefa ba son sa take yi ba shi yake kiɗin sa yana rawar sa ga inda ake son sa amma ya kwashi jiki ya tafi in da ba a son sa. Ita dama tun da Areefa ta shigo cikin Company nan gabadaya taji bata kwanta mata ba sosai take ji a ranta akwai abin da zai faru don ta lura ita ma Areefa ba wai aiki ne kawai ya kawo mata ba har da wani KUDIRI nata na daban. Tsaki taja kadan kafin ta gyara zaman rolling din da tayi wa dan kwallin jallabiyar dake jikinta sosai ta gyara zaman glass din dake fuskarta kallo daya kayi mata ka san ita ma ba baya b wajan kyau da kirar jiki fara ce amma ba can sosai ba. A hankali ta turo kofar Office din ta shiga zuciyarta na bugaawa da halin tsoro don bata san abin da zai je ya dawo ba bata san yarda Dr.Erena zai karbeta ba ta san ya zai anshi abin da za taje masa dashi ba. "...Bobby karka sake ka bata min rai kayi kawai abin da nace da kai ba wai ka kai shi can in da ba a dawowa ba a,a kawai so nake yi yaji a jikinsa ya san har yanzu Dr.Erena yana nan a yarda ya sanshi ba wai canzawa yayi ba". Tana kokarin buɗe baki tayi sallama ta tsinkayi muryar Dr.Erena ya na fadin haka ai mutuwar tsaye tayi idanuwanta a warwaje lokaci guda jikinta ya shiga ɓari kamar wacce akayi wa wankan ruwa mai tsanani sanyi gumi ya shiga tsantsafo mata a jiki lokaci guda duk taji jikinta ya shiga narkewa da duk wani kudiri da buri da ta zo don cimmawa a hankali ta shiga jan numfashi tana mamakin kalaman Dr.Erena bata taba zaton haka yake ba bata taba zaton akwai rashin imani har haka ba a ransa. A hankali ta shiga kokarin juyawa don ficewa amma zuciyarta tana hanata akan kudirin da ta zo dashi sosai taji komai ya fara canzawa tsoro da fargabar da take yi ya ragu sosai zuciyarta na kara mata jarumta akan kawai taje ai mai nema ba ya rasawa ita fa abin da ta zo yi daban maganar da yake yi bai shafe ta ba kuma ba ta san abin da yasa yace haka ba. Da wannan tunanin ta shiga saita kanta gabanta na faduwa kadan kadan. Sallama tayi tana mai cusa kanta cikin Office din tsaye ta hangeshi yana kai kawo fuskarsa da murmushi wanda daka kallashi zaka gane na mugunta juyowa yayi jin sallamar da kayi dubanta yake yi cikin wani irin yanayi kafin ya kau da kan sa. "Sannu Sir". Ta fadi da kokarin dauko jarumta ta azawa kanta ansawa yayi a ciki kafin ya dube ta ba yabo ba falla sa. "Lafiya me ke faruwa ne Mufeeda?". Sosai taga yayi mata kwarjini a idanunta gabanta taji yana bugawa wata irin burgewa take jin lokaci guda tana karuwa akan Dr.Erena juya idanunta ta shiga yi tana faman yak'e kamar wacce bata da gaskiya. Dubanta ya shiga yi da wani irin yanayi na tuhuma kafi ya tako inda take tsaye. "Akwai wani abu ne?". Ya fadi yana kureta da kallo da ya kusan narkar mata zuciya da gangar jiki. A hankali ta shiga motsa baki zuciyarta na tsallen tsoro akan yarda zai anshi lamarin. "Sir, dama akan maganar Areefa ce". Dan yatsine fuska yayi kafun yace. "Me ya faru da Areefa din wani abu tayi miki ne?". Girgiza kai tayi kafun ta ja numfashi mai tauri tana jin yarda wani abu da ya tokare mata kirjiya ya sauka. "Gaskiya Sir. Ban yarda da ita ba jikina sam! Bai kwanta da ita ba tun da ta zo Company din nan sosai nake ji ajiki kamar ba alheri bace a gareka da ma mu kafatanin ma'aikatanka...". Hautsine wa fuskarsa ta shiga yi da wani irin bacin rai idanuwansa suka shiga kaɗawa da tsananin haushi kafin ya dube ta sosai da sosai yana faman hirji kamar wani kumurci. "Me kike cewa Mufeeda Areefa din ce ba alheri ba Areefa ce kike jifa da wadannan kalaman naki kina da hankali kuwa anya ba wani abu kika sha ba wanda ya rabaki da duniyar hankali gaskiya bana zaton kina cikin hayyacinki na lura ke ma kin fara yan kurɓe-kurɓen nan na yan matan wannan zamani in ba haka ba ina ruwan ki da ita mai ya shafe ki da ita rayuwarki daban ta ta daban don haka tun wuri tun muna kallo juna a mutunce ki fice mani daga Office tun kafin na keta miki rashin mutunci.". "Am...amma Sir. Daka tsaya ka fuskance ni gaskiya ce fa nake sanar da kai...". Wani kallo ya watsa mata kafun ya shiga nuna ta da hannu. "I Say Get Out! tun kafin nayi miki abin da baki taba zato ba". ware idanu tayi sosai jin furucinsa ya taba mata zuciya amma sai taki barin haka yayi tasiri a zahirancen cikin jarumta ta sake dubansa murya alankwashe. "Sosai na fuskat kamar akwai wata alaka a tsakanin kai da ita Sir hakan kuma bai dace ba sam ya kamata ace ka nemi mace mai daraja mutunci a matsayinka na mutum mai daraja da mutunci mutane da yawa yanzu kallon wani daban suke yi kamata ganin alakarka da Areefa...". "Mufeeda! Which can of nonsense kike kokarin gaya mini me kike nufi dani me kike so ki ce da nine akan Areefa ya kamata tun wuri ki gyara kalaman ki kuma ki sani indai akan Areefa ce kika zo kina yi mani wannan haukar wallahi tallahi gaf! kike da barin Company din nan". Gwalo idanu tayi waje sosai zuciyarta na wani irin raɗaɗi da zafi komai take ji na jikinta yana canzawa sosai take jin komai nata kamar ba nata ba kalaman Dr.Erena ba karamin taba mata zuciya sukayi ba ji take kamar ta daura hannu aka ta kurma ihu bata san ya zatayi ba bata san me zatayi Dr.Erena ya kalle ta a mutunce ba bata san hanyar da za ta bi ba domin ya kulata ya anshi tayin da take masa ya sota kamar yarda ta kamu da son sa a filin duniyar zuciyarta sosai take son sa so bana wasa ba tana kishinsa ba ta son duk wata mace ta ga tana kusantarsa sosai tashiga tashin hankali lokacin da ta ga Areefa ta fado rayuwarsa. Wasu kwalla taji suna neman zuba mata da sauri ta dauke su ba tare da Dr.Erena ya gani ba amma sai dai tayi shuka a idon makwarwa domin kuwa duk motsinta akan idonsa take yi da mamaki yake dubanta sosai hawaye da ta shafe ya kara sanya shi a mamaki sosai sakanni ya dauka yana kallonta kafun ya ce da ita cikin muryar tuhuma. "Hawaye Kuma me yayi zafi shi ba wuta ba Mufeeda me yake damun ki wani abu akayi miki ne Pleaae Leave my Office ba zan dauki wannan haukar taki ba kin ji ko I need to be alone ba na son abin da zai kawo mani ciwon kai don ba dauka zan yi ba". Murmushi tayi wanda ya fi kuka ciwo sosai take jin bakin ciki da takaici na rashin darajawa da Dr.Erena yake nunawa akanta sosai take ganin rawar kanta da gangacin da zuciya tayi mata na son wani wanda bai son tana yi ba ga ta yanzu a gaban shi amma yana nuna ita da banza duk daya bata san mai ya sa haka ba ta san dai SONE SILA wanda bai yi mata adalci ba bai dace ace yayi mata haka ba bai kamata ace AKAN SO tana kuka ba kukan ma akan wanda ba tayi tsammanin zuciyart za ta so shi ba ko a mafarkin ta ba ta taba zaton zuciyarta zata dauko mata son Dr.Erena ba ta kawo mata tun da ta fara aiki a Company tun ranar da ta daura idanuwanta akan sa taji ta kamu da son sa amma bata san ta yaya zata bayyanar son da take masa ba a gareshi domin sosai da sosai yake mata girma da kwarjini a idanunta. Ba ta zaton za ta iya barin nan batare da ta amayar masa da abin da take ji game dashi ba bata zaton zata iya daukar gangar jikinta ta fice daga cikin Office din nan batare da ta bayyana son da take masa ba ko da kuwa hakan zai sanya ya kore ta daga Company din nan. Ba za ta iya cigaba da dakon son sa ba tana bukata zuciyarta ta sarara mata da tashin hankali da take samun kanta kullum a ciki runtse idanuwanta tayi kirjinta cike fargaba da tashin hankali mara musaltuwa tana jin yarda kirjinta ke bugawa da sauri-sauri motsa laɓɓanta ta shiga yi kanta take ji yana juyawa amma haka ta kinkimo jarumtar duniya ta daurawa kanta. "Dr.Erena...". Ta fadi tana jan wani numfashi mai tauri gaske shi kuwa dubanta yake yi da mamaki cike da fuska jin a RANA DAYA Mufeeda ta kira sunansa abin da bata tabayi ba tsayin lokacin da ta fara aiki sosai ya natsu yana dubanta kafin ya ja kujera ya zauna. "Na jima a duniyarka ina shawagin son ka amma sam baka lura da haka ba, na jima ina jiyar zuciyata da tayi gangancin daukar sonka ta azawa kanta, na jima ina kwaɓarta amma ta ki ji tayi nisa a sonka, na jima ina sanar da ita cewa ba mu dace ba amma bata ga hakan ba ta nuna min so ba ruwansa da haka, Dr.Erena naji ma ina son ka so mai tsanani sosai nayi zaton za ka gane in da na dosa amma ina sam hankalin ka bai kai nan ba maganar gaskiya ina son ka kai ne namiji na farko a filin duniyar nan da zuciya ta tayi amanna dashi a fannin so ban san ya zan kwatanta maka ba amma ka sani ina son ka so mai ansa suna so". Zabura yayi daga kan kujerar da yake zaune idanuwansa cike da tulin mamakin maganganun Mufeeda hannu ya shiga nuna ta dashi yana jan numfashi kafun ya saki wata dariya wacce ta kaɗa 'yan hanjin Mufeeda sosai lokaci guda taji gabanta ya yanke ya fadi runtse idanu tayi wasu hawaye suka zubo ta kasar Glass din da ke fuskarta kafin ta shiga haɗe hannayenta waje daya tana Rolling din su. "You Love Me? For God Sake! Mufeeda kina cikin hayyacin ki kuwa kin san waye Dr.Erena kuwa da kike daukar wa kan ki wahalar son sa to maganar gaskiya ba zan boye miki ba bana tunanin zan iya zama nayi soyayya dake bake ba ma hatta WATA MACE daban bayan Areefa bana zaton ko kallon arzuki zan iya yi mataa ya kamata ki san wani abu mace bata gabana mace daya na taba so kuma nake burin zama da ita ita ce Areefa ita ma ban san ya akayi zuciyata ta kamu da son ta ba a RANA DAYA ba zato ba tsammani naji KIBIYAR AJALI ta son ta ta cakar min zuciya wanda har zuwa wannan lokaci na kasa zareta sai kara lumewa take yi cikin zuciyata da duk wani gurbi na cikin ta". Dubansa take yi da duk idanuwanta da suka kaɗa sukayi jajir fuskarta har tana canza kala izuwa ja sosai take jin duniyar nayi juya mata da duk wasu kalaman Dr.Erena da take jin su kamar saukar garwashin wuta. Numfashi take ja da take jin sa kamar ta na jan barkono izuwa kanta dama cikin ta sosai take jin duk wani sashi na jikinta na narkewa kamar zata watse a kasa dan yatsanta daya ta kai baki tana cizawa domin tabbatar da abin da yake faruwa da ita gaskiyane ba a mafarki bane yau ta kara tabbatar wa da maganar hausawa na cewa SON MASO WANI koshin wahala ne ta tabbatar da yau Dr.Erena baya tare da ita At All baya gayyatarta a filin duniyarsa bai ma san tana yi ba. "Na lura da abin da kika zo dashi akan Areefa duk kishi ne kina tunanin son da nake yi mata zai bari na dauki abin da ki ka zo mani dashi a gaske to ko da kuwa gaske ne ba zan dauka ba Areefa mace ce da nake so so mai garman gaske wanda bana zaton a filin duniyar nan akwai macen da zan iya yiwa ko da kwatar son ne don haka fice mani daga cikin Office". Ya fadi yana mai yi mata nuni da hannu fuskarsa a murtuke kamar bakin hadarin da ya gangamo yake kokarin zubda ruwa. "Dr.Erena MENE NE LAIFIN ZUCIYA don ta nuna so da kulawa akan abin da take so bana zaton son da nake yi maka zaka yi masa fatan KARKON KIFI ka sani so nake yi maka son da ban taba yi wa wani ɗa namiji ba a filin duniyar nan ya kamata ace ka girmama son da nake yi maka ka dauke shi da daraja ka killace shi a zuciyarka a wani fili ko ya ya ne...". "Are U At Of Your Sense Mufeeda kina da hankali kuwa wacce irin magana ce haka kike fadi wani irin hauka ne haka ina so dole ne nace bana yi na ce bana sonki leave alone mana". Murmushi ta saki mai ciwo kafun ta zare Glass din dake fuskarta idanuwanta da suke rine suka bayyana sosai take duban Dr.Erena da yake mata kallon wulakanci da raini laɓɓanta ta ciza. "Karka yi tunanin don na furta kalmar so a gareka zai baka lasisin wulakanta ni, karka yi tunanin don buɗe baki na sauke aji na da daraja ta ta 'ya mace za ka wulakanta ni ka sani ba aibu bane san nan ba zubda mutunci bane don mace ta buɗe bakinta ta fadiwa ɗa namiji tana son sa ba san nan haka ba yana baiwa ɗa namiji dama bane don ya wulaƙanta 'ya mace don ta nuna tana ta son sa ba duk macen da zata iya buɗe baki tana cewa namiji tana son sa ba abin kunya bane kuma ba abin a wulakanta ta bane domin tayani don ceto kanta da halin da zata fada ka san wannan Dr.Erena karka yi tunanin son da na nuna ina yi akan ka zai baka damar tozartani ka wulakanta ni daraja da martaba ta tana nan ba abin da ya ragu sannan ko a duniyar masoya na san nayi abin kwarai wanda da yawan mata ba sa yi sannan kuma kamar yarda mata suke tsoro halin da ka nuna min da tozarci da wulakanci don kawai na nuna ina son ka ba laifi na bane laifin zuciya tane wacce ba ƙashi gareta ba". Dubanta ya sake yi a wulakance domin sosai zuciyarsa tayi zafi da kalamanta motsa baki ya shiga yi yana kokarin magana ta daga masa hanni. "Ba sai ka daka min tsawa koka koreni kamar wata mara 'yanci kai ba yanzu zan bar maka Office din ka". Tana fadin haka tayi hanyar fita daga Office har ta rike Handle din ta juyo ta dube shi sosai kafun ta kau da kai tare da ficewa daga cikin office din tana kokari hau benen da zai kai ta kasa ita kuma Areefa na sako kai saura kadan suyi gware nan suka shiga kallon kallo a tsakanin juna su fuskar Mufeeda cike da kunci da bakin ciki kallon Areefa take yi da wani irin yanayi kafun ta kau da kai gami da jan tsaki ta wuce ita dai Areefa bin ta take yi da kallo ganin yanayin da take ciki kamar akwai abin da take damun ta musamman idanuwanta da suka kaɗa sukayi jajir kafaɗarta ta daga cikin nuna halin ko in kula kafin ta isa ta tura kofar cikin Office din. Tsaye ta same shi yana kai kawo hannayensa goye a bayan sa motsin shigowar tane ya sanya shi tsayawa yana jan numfashi fuskarsa a daure kamar hadari. A hankali ta isa ta zauna tana mai daura kafa daya kan daya bakinta dauke da cingum tana faman taunawa idanuwanta akan Dr.Erena kallon sa take yi da wani irin yanayi mai haifar mata da ɗaci a zuciyarta sosai take dubansa da damuwar da take fuskarsa a ranta take fata dama ya dauwama a haka yaƙe ta saki kafun ta kaɗa idanuwanta. "Me ke faruwa ne Dr.Erena?". Sai a lokacin yaja numfashi mai girma ya na huci gami da runtse idanuwansa dubanta yayi kafun ya ja kujera ya zauna. "Wannan mai kalar haukar ne za tayi mani akunyanci bata san na fita da duk tashencin ta ba". Cikin rashin fahimta ta yatsine fuska cikin son karin bayani. "Wai fa zuwa tayi tana sakin wasu banzayen kalamai kafun daga karshe ta dire da cewa wai ni take so ki ji fa wata wauta da kalar hauka". Fakare tayi tana kallonsa tana karantar yanayin sa mamaki ya cikata ta yarda Mufeeda ta iya jefa kanta son wannan mugun mutumin mara tausayi da imani ita kam bata ga abin so a jikinsa ba bata ga abin burgewa a gareshi ba har da Mufeeda zata zo tana fada masa tana son sa har ya samu damar ci mata mutunci ya wulakanta ta ko da yake kila kudin da yake dashi ya ruɗeta in kuwa haka ne Mufeeda bata yi wa kanta adalci ba da tayi sake ta fada motar kwadayi ta dire a tashar wulakanci da cin mutunci. "Ni ban ga abin ta da jijiyoyin wuya ba don tace tana son ka ai ta dace ace kai ma ka anshi son da take yi maka duk macen da zata iya zuwa ta ce tana son ka ai bata cancanci wulakanci da tozaryawa ba duk da dai ku mafiyawancin maza haka kuke in har kuka ga mace ta mutu akan son ku shikenan kun samu hanyar wulakanta ta da cin zarafin ta iri-iri". Murmushi yayi lokaci guda kafun ya motsa laɓɓansa. "Bana tunani haka zata kasance tsakani na da ke Areefa so daya nake yi kuma akan ki yake bana zaton akwai wata mace da zan so bayan ki akan ki na fara so kuma akan ki zan gama so ki san wannan". "Uhmm haka dai kace aiku dama haka kuke maza akan mace akwai iya dadin baki musamman in duniya na yi muku biyayya ba abin da ba za kuyi wa mace ba". "Areefa na lura kamar kina goyon bayan Mufeeda da ne ko baki jidadin abin da nayi mata ba". "Ko daya wallahi amma dai ka sani mace mace ce ko min lalacewarta don haka ka kula mace ba yar wulakanci bane ita mai daraja ce da kima duk da dai wasun mazan ba su dauki mace a bakin komai ba sun mai da ita kamar riga lokacin da suke ra'ayin ta za su saka ta da sun gama kuma su cire su ajje ita da banza duk daya". Mikewa tayi tana mai daukar jakarta ta dubi Dr.Erena da ya saki baki yana ta faman murmushi idanuwansa akanta kafun ya mike shima. "Ya haka Areefa ina zaki daga zuwanki kuma Please ki zauna mana akwai maganar da nake so muyi dake mai muhimmanci ce". "At this Time bana tunanin zan iya zama kuma ina da abin yi gaskiya". "Please mana Areefa". Juya idanu tayi kafun ta dube shi cikin gyaɗa kai ganin haka ya sanya shi komawa ya zauna yana mata nuni da ta zauna ita ma ba musu ta zauna yana ma kallonta kallo na sosai da sosai kafun ya ja mumfashi. "Areefa maganar gaskiya ya kamata ace kin ce wani abu akan alakar dake tsakaninmu ya kamata ace kin motsa motsawarki kawai nake buƙata a yanzu". Ci rashi bawa zancen nashi muhimmanci ta dubeshi kafun ta motsa laɓɓanta cikin ɗacin zuciya. "Ina jin ka me kake nufi?". Sai da ya sosai ƙeyarsa kafun ya saki murmushi na sosai da sosai. "Maganar aure mana ya kamata ace mun tsayar da magana a wannan lokacin...". Da sauri ta daga masa hannu tana mikewa kan kafafuwanta zuciyarta take ji tayi wani bugawa da tashin hankali mai girman gaske jin zantukan nashi take yi kamar saukar aradu ƙwanyarta taji tana juya a hankali ta dube shi. "Please ka bari za muyi waya in na koma gida kaji komai zai yi settling a cikin kan kanin lokaci". Tana gama fadin haka ta fice daga Office din cikin sauri kamar wacce zata kifa haka take ji komai taji lokaci guda ya canza mata da tashin hankali mai girma kunnuwanta take ji ba za su iya daukar kalamansa ba masu dauke da kunci da bakin ciki tafiya take yi har ta sauka kasa ta isa in da sashin ta yake komai ta kammala a hanzari ta zare key din motarta ta fice daga cikin reception din tun kafin ta isa in da motar ta take tayi mata key ta buɗe baya ta isa ta shige ta haɗe kanta da sitiyari tana mai da numfashi a hankali kanta take ji yana sarawa da karfin tsiya kamar zai rabe gida biyu sai da ta shafe lokaci mai tsayi kafin ta yiwa mota key ta fizge ta cilla ta saman titi ta shiga zabga gudu kamar wacce zata tashi sama burin ta kawai ta ganta a gida ko ta samu tayi saita kanta sosai take jin tashin hankali na tunkaro ta sosai take jin ranta na kara baci duk lokacin da suka hadu da Dr.Erena don dole kawai take zama dashi da umarnin Hajiya Layla. ********* Tun da ya doso Muhabbir Coffee yake jin gabansa na yankewa yana faduwa lokaci lokaci hakan na karuwa sosai yaji a jikinsa akwai abin da ke kokarin faruwa dashi. Parking yayi bayan yashiga wajan yayi oda din duk abin da yake bukata ka kawo masa a hankali yake kai Coffee bakin sa yana kurba har zuwa lokacin jikinsa bai daina sanar dashi wani abu dake kokarin faruwa dashi ba tun yana daukar lamarin da sauki har yaji zuciyarsa tana kara azalzalarsa da yabar wajan A hankali ya mike ya dauki wayarsa da key din sa bayan ya biya kudin abin da yayi oda ya doshi in da motarsa take ajje ya bude ya shiga ya zauna bayan kulle yana kokarin yi mata key yaji an dorasa masa bakin bindiga ta bayan kansa zare idanu yayi a firgice yana kallon mutane biyun da suke bayansa zaune ta glass din gaban motar. "ja motar muje". Daya daga cikin su yace dashi murya a buɗe gabadaya kamar saukar markaɗe. Jikin rawa ya shiga yi jin abin da suka ce dashi ware ido yayi yana kokarin juyawa ya dube su laɓɓansa na motsi daya daga cikinsu ya daka masa tsawa cak! ya tsaya da maganar da yake kokarin yi jikin sa na ƙyarma sai faman ambaton sunan Allah yakeyi. A hankali yayi wa motarki bayan ya yi ribas ya fice daga cikin wajan. In ba wai kasan abin da yake faru a cikin motar ba ba zaka iya cewa komai ba dubin gabadaya glass din motar mai duhu kuma a zuge yake. Suna fita daga cikin wajan suka shiga nuna masa hanyar da zai bi a hankali a hankali suke tafiyar har suka fara ficewa daga cikin gari nan Alhaji Abdulwahaab ya kara ruɗewa ganin suna tun karar daji da sauri yayi kokarin taka burki amma jin bindiga a keyarsa ya sanya shi kara wuta cikin hanzari jikinsa na rawa domin ya tabbatar wadannan mutanan barayi ne ko kuma yan satar mutane. Daji sosai suka yanka sai da yashiga cikinsa sosai sannan suka ce yayi parking a hanzarce yayi sannan ya juya yana kokarin kallon su daya daga cikin su ya buga masa kan bingida a gefen fuska wanda hakan ya sanya shi sakin kara gami da yin lif! jikin kujera kamar wani mara lafiya wajan da suka dokar masa lokaci daya ya fara fiddo jini. Gabadayan suka buɗe suka fito dayan su ya ja kofar gaban ya buɗe ya fizgo Alhaji Abdulwahaab zuwa waje ya baje akasa kansa na buguwa da gefen motar wata irin kara ya saki gami da ambaton sunan Allah numfashi kawai yake ja a hankali gabadaya ya gama shiga tashin hankali mai tsanani dagowa yayi cikin matsanancin yanayi yana duban su ganin su yake yi suna kasuwa bibbiyu idanuwansa suna lumshewa a hankali yana buɗe su bai ankaraba ya sake ji an kai masa wani wawan naushi a fuska an daki goshinsa da kan bindiga nan ya baje a sume bai sake sanin in da kan sa yake ba. Duban juna sukayi suna masu sakin wata mahaukaciyar dariya kafin su tafa hannayensu a hankali suka fara tafiya suna ficewa daga wajan shikuwa Alhaji Abdulwahaab bai ma san in da kan sa yake ba. Ya dauki lokaci mai tsayi can wajan magrib sanyin yamma ya kaɗashi ya farka a wahale yana kokarin buɗe idanuwansa amma jin su yake yi kamar ba a jikinsa suke ba dafe kan sa yayi sosai yana mai kara runtse idanuwansa lokaci daya ya buɗe su duhun daren da ya fara shigowa shi ya an karar dashi da sauri ya tashi zaune ya juya yaga motarsa hannu ya saka ciki Aljihu wayarsa yaji da sauri ya zaro yana dubawa 6:50pm shida da minti hamsin ya gani a hankali ya shiga kokarin tashi amma tsamin da jikinsa yayi ya hana shi kokarin da yake yi rarrafawa yayi har ya isa wajan motar ya dafata sannan ya mike yana faman cizon laɓɓansa buɗe motar yayi ya shiga a hankali yana faman numfarfashi yakeyi zama yayi sosai yana jin yarda bayansa ke amsawa da ciwo mai tsanani cikin dauriya yayi wa motar key Allah ya taimake shi ta ta shi ajiyar numfashi yayi mai karfi a hankali ya shiga yin ribas har ya juya hanyar da zata fiddo shi daga cikin daji. Sosai ya fita daga cikin daji ya shiga gari daidai wani Super-Market ya tsaya ya daga kansa sama daidai wani shago da yake zaton clinic ne haka kuwa akayi KAMALA CLINIC ya ga an rubuta da dan hanzarin sa ya buɗe ya fito ya doshi wajan bayan yayi sallama ya shiga nan ya yi musu bayanin abin dake faruwa wani daga cikin ma'aikatar wajan ne ya zo yayi masa komai da ya dace har da allurai sai daya sha Kafun ya fito ya dauki hanya zuwa gida zuciyarsa cunkushe da godiyar Allah da lamarin ya tsaya a haka ba tare da sunyi masa wata illa sosai ba. *_KAMALA MINNA_*😘😘😘 [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA TALATIN DA SHIDA. Juyi kawai yake yi saman faffaɗar gadonsa da ya kusan cinye rabin dakin numfashi yake ja a hankali zuciyarsa na wani irin kartawa. A hankali ya mike yana kai kawo a tsakiyar dakin gumi mai tsananin zafi sai tsantsafo masa yake yi a goshi lokaci-lokaci yake runtse idanuwansa ba abin da yake hangowa sai Huzaif da ya rike hannun Mariya sosai yaji zuciyarsa na zafi da zugi wani katon abu mai nauyi yaji ya zo masa zuciya ya tsaya cak!. Bai san abin dake damun sa ba a daidai wannan lokacin zuciyarsa sosai take son firgita masa tunani game da Mariya sosai yake jin wani fili mai girma ya buɗe a zuciyarsa ba abin dake yada zango a cikin sa sai lamarin Mariya sosai yake hangowa a ranar da ya fara ganinta bayan shekaru hudu da suka shuɗe ba tare da ya sanyata a idanuwansa ba. Runtse idanuwansa ya sake yi a karo na ba adadi kafin ya shiga taka kafafuwansa a hankali yana mai isa toilet din sa ruwa ya watsa domin ko zai samu sa'ida a zuciyarsa dama gangar jikinsa gabadaya. Yana cikin goge sumar kansa da shawul wayarsa dake yashe gefen gadonsa ta dau Ringing ya tsine fuska yayi kafin ya dubi wayar cikin halin-ko-in-kula yana mai jan guntun tsaki sai da wayar ta tsinke sau biyu kafin a na uku ya kokarta zuwa ya dauka new number ga ni kuma bata najeriya bace shiru yayi yana tunanin inda number din ta fito amma ya kasa cankowa yayi kamar zai katse sai wata zuciyarsa ta bashi damar dagawa a hankali ya latsa madannin yana kaiwa kunnansa mai makon ya rike da hannunsa sai ya ƙi sai ya makale ta a kafaɗarsa. "Dr.Karami". Yaji muryar ta doki dodon kunnuwansa da sauri ya yarda shawul din dake hannunsa ya dago wayar daga kunnansa yana duba number din sosai mamakin murya da yaji yake yi sosai gabansa ya buga kadan don yasan shi mai laifi ne sau ba adadi yana kiransa yana kin dauka wanda bai san dalilin ba a hankali ya ciji laɓɓansa yana mai da wayar kunnansa. "Uhmm!". Ya fadi da dan sauti a muryarsa. "Ka kyauta kaji Dr.Karami...". Runtse idanu yayi kafun ya motsa laɓɓansa. "Please Sorry My Dr.Vijay kasan dai ba haka kawai zan shan yaka ba dole sai da dalili". "Ban yarda ba kawai kace mani wulakanci ne ya tashi ko abin da ba halayyakar baka...wai shin ma me ya zaunar da kai ki dawo wa aiki ne har yanzu 3weeks left fa haba mana ya kamata ace duk abin da kake yi izuwa wannan lokaci ka kammala shi ka dawo". Runtse idanu Dr.Karami yayi yana jin yarda zuciyarsa ke sake hautsinewa da wani irin yanayi mai girman gaske na tashin hankali ba ya zaton zai koma aiki ba tare da komai ya daidai ta ba, ba ya zaton zai koma Delhi a yanayin da yake a yanzu ko yace zai koma to tabbas karya yayi domin kuwa ko yaje din ganga jikinsa ne kawai zata je can din amma zuciyarsa da ruhinsa suna nan nisawa yayi kafin ya fesar da huci mai zafi. "Ina cikin wani yanayi ne mai matukar girma Dr.Vijay a halin da ake ciki yanzu ban san ranar dawowa ta aiki ba in har ba wai komai ya zama Normal bane". "What?!. Me kake kokarin cewa dani Dr.Karami anya kana hayyacin ka kuwa aikin naka kake mai dawa haka kana masa halin ko in kula meye ya same ka har da kake wannan ikirarin haka ya kamata gaskiya ka sauya tunani tun wuri kuma ya kamata ace ka dawo aiki at this time domin ana bukata ka". "Ba zan iya ba". "Kan wani dalilin?". "Kawai dai ba zan iya dawowa a yanzu ba domin akwai abu mai girma da nake so ya zama normal in har ba wai ya zama normal din bane to gaskiya bana tunanin ko na dawo zan iya wani abun kirki". "Shikenan Allah ya kyauta". Abin da Dr.Vijay ya fadi kenan da damuwa a muryarsa shi kansa Dr.Karami ya lura da haka sai dai ba yarda zai yi a matakin da yake a yanzu ba ya tunanin zai iya komawa Delhi sauke wayar yayi bayan sun yi Sallama jiki a mace ya zube bakin gadon kamar wani kayan wanki hannunsa ya saka ya dafe kansa da yake jin yana yi masa wata irin sarawa kamar zai rabe gida biyu runtse idanuwansa yayi kafin ya buɗe su a hankali. Sosai yake jin zuciyarsa na sonta sosai yake ji duk jikinsa na aiki ne da sosai yake jin zuciyarsa nayi mata ya jima yana karyata kansa akan cewa son ta yake yi ya jima yana jin zuciyarsa na sanar dashi amma ya ki ansar lamarin sosai yayi kunnan uwar shegu da komai ba tun yau ba lokaci mai tsayi da ya shuɗe zuciyarsa tana kawo masa abubuwa masu matukar girma a game da ita amma bai yi AMANNA ba. Bai san ya zai yi ba bai san ya zai fuskance ta da wannan lamarin ba sosai yake jin wani iri a zuciyarsa sosai yake hango rashin nasara baya tunanin in ya tunkare ta da wannan lamarin zata ansheshi har ta bashi fili a zuciyarta. Fushi take yi dashi fushi na sosai da sosai bai san mai yasa ba ya sani har da laifin sa laifin sa mai girma ne a gareta wanda bai san ya zai wanke kansa ba a idanuwanta ta ki yarda dashi taki bashi lokacin ta su zanta gudun sa take yi sosai ta ke kin haɗa ko da hanya dashi ne sosai yake bibiyarta amma bata bashi lokaci yayi iya yin sa saboda ita ya baro aikin sa saboda ita ya zauna har tsayin wannan lokacin tun da ya fara aiki bai taba zuwa ya zauna a kasar nan ba mai tsayi sai a dalilinta a dalilinta komai nashi yake canzawa wanda bai yi zato ko tsammani ba zuciyarsa ta dade da narkewa da duk wani lamarinta ruhinsa ya jima da daskarewa da duk wani abu nata kwanyarsa ta jima da buɗe fili mai girma na tunaninta. A tunaninsa ba ta kai matsayin da zai so taba, a tunaninsa ba ta kai matsayin da zai tsaya ya nuna yana son taba, a shekarunsa gani yake yi kamar ba su dace ba, gani yake yi kamar sun bambanta a wajaje da dama sai dai wani abu da yake kokarin ruguza duk wani tunaninsa a lokaci kankani ganin yarda ta canza komai na ta ya sauya ta koma masa mace mai ansa sunanta mace ta ko wani fanni sosai yake ji a ransa yayi wauta a can baya tunaninsa bai yi masa adalci ba da ya tunano masa rashin dacewa tsakaninsa da ita sai yau ya kara tabbatar wa SO SHU'UMI NE so ba ruwansa da girma ko yarinta a ko wata zuciya zai iya sauka ya buɗe filinsa yayi yarda yake so da zuciyar. Numfashi ya ja mai tauri kafin ya fesar da huci mai zafi a hankali ya mike ya shiga shiryawa cikin riga da wando rigar mai dogon hanni Milk-colour sai blue din wando mai haske kayan sun yi matukar ansarsa suka kara fito da tsarin halittarsa ta mazantaka kallo daya zakayi masa ka gane Allah yayi halittar ɗa namiji a wajan mai ji da kansa ta ko wani fanni. Sosai ya feshe cikin sa da turare mai dadin kamshi dakin kansa sai da ya dauki kamshi na ban mamaki kamar anyi barinsa. Bayan ya kammala ya dauki Key din motarsa da wayarsa ya fice can parking Space ya nufa ya fiddo motarsa sai da ya gama kare mata kallo kafin ya buɗe ya shiga yayi mata key a hankali ya ja ta ya fice daga harabar gidan ya cilla titi. London Streat unguwar ya nufa in da gidan mahaifiyarsa yake tuki yake yi a hankali a jikinsa yake ji kamar bashi da lafiya sosai yake jin ko wani sashi na jikinsa kamar an doddoke masa cikin wannan yanayin ya isa gidan Horn yayi mai gadi ya buɗe masa Get Babban gida ne sosai kallo daya zaka yi masa kasan masu gidan akwai farcen susa ko wani sashi ka kalla tsaf yake Parking yayi ya fito bayan sun gaisa da Malam Audu mai gadi sannan ya nufa hanyar Falo din da sallama a bakin sa ya tura ya shiga ba kowa a falon sai Tv dake ta faman aiki yawatawa ya shiga yi da idanuwansa cikin falon da yake ta faman tashin kamshin turaren wuta a hankali ya ja numfashi yana mai sakin yak'e kamar wanda akayi wa dole da sauri yayi hanyar dakin mahaifiyar tasa don ya tabbata tana ciki. Zaune ya tadda ita bayan yayi mata sallama ta ansa shi fuskarta da murmushi mai girma kallo daya zakayi mata ka tabbatar da ita ce mahaifiyar tasa suna kama sosai sai dai shi Dr.Karami ya fita hasken fata saboda hasken fatar mahaifinsa ya biyo kama ce dai ya dauko ta uwa sak! A hankali ya isa gareta shi ma fuskarsa da murmushi kan salayar da take kai ya samu guri ya zauna ya na daura kansa a kafadarta shafar kansa tayi kafin ta rufe littafin Husnul-Muslim dake hannunta. "My Son ya akayi ne?". Margaya kai yayi kamar wani karamin yaro kafin ya dago kansa ya dubeta. "Ba komai Mami kawai dai yau bana jin dadin jikin nawa ne sosai". Zaro idanu waje tayi kafin ta furta. "Yaa Allah da fatan dai ba wani abu bane yake damun ka". Girgiza kai kawai yayi kafun ya mai da kan nasa jikin kafadarta. Wani numfashi taja mai kwari kafin ta dubi Dr.Karami sosai fuskarta da wani irin yanayi mai girma na damuwa. "Hisham". Ta furta kamar bata so ba da hanzari ya mike yana dubanta jin ta ambaci sunansa sak! Wanda ya manta rabon da yaji ta kira shi da hakan sosai yake kallon ta jikinsa da wani irin yanayi gabansa ya ji yana bugawa a hankali. Kau da kai tayi daga kallonsa. "Na fara gajiya Hisham abin dai da baka so shi zan fadi ban san adadin lokutan da nake zaunar dakai muna irin wannan maganar ba ban san adadin lokacin da na dauka wannan lamarin na damuna ba abin ya fara shanlake tunani tun kafin rasuwar mahaifinka ake abu daya amma har yau babu wani lamari to maganar gaskiya in har ba so kake yi nima na mutu da wannan burin ba to ya kamata ace kayi wani abu akai ba wai takura maka nake yi ba abin da zai kuftar da kai daga fadawa halaka nake gujewa ba wai ina zargin ka bane da komai Hisham amma ya kamata ace a irin wannan shekarun naka yaci ace kana da mata har da 'ya'ya duk da dai komai na rayuwar nan sai Allah ya sa zai tabbata san nan yake tabbata". Shiru yayi kansa na wani irin juya masa gabadaya yake jin komai na kara hargitse masa musamman yanayin da ya ga mahaifiyarsa a ciki a yau din nan ya san ta kai makura amma shi kam bai san ya zai yi akan maganar auren nan har yanzu bai jin akwai wacce zai iya zama da ita a filin duniyar nan a matsayin mata ba shi akaran kansa yana mamakin rashin aurensa bai san dalili ba bai san mai yasa sam a shekarun da ya kwashe na girman sa bai ji yana da muradin aure ba domin zuciyarsa har yau bai ji ta kamu da son wata 'ya mace ba... Shiru yayi jin zuciyarsa na karyatashi da abin da yake fadi wanda ya tabbata a yanayin da yake ciki yanzu komai ya sauya komai ya canza sosai yake jin so a cikin zuciyarsa son ma akan wanda bai taba tsammani ba. "Hisham kai kadai ne ɗan mu a duniyar nan kai kadai Allah ya ba mu duk da muna son 'ya'ya haka muka hakura da hukuncin Allah kai ya kamata ka share mana hawaye na 'ya'ya bila adadin amma kuma ya kamata ace kai a bangaren ka kayi aure ka hayayyafa domin Ubangiji yayi alfahari da kai nima nayi alfahari da kai mu ba muyi ba ya kamata ace kai kayi Hisham a maganar gaskiya shekarun sun kai matakin da ya dace ace ka ajje iyali in har ba so kake yi ka koma ga mahaliccin ka a haka ba ba abinda ka rasa kana da arzuki daidai gwargwado kana da aikin yi ba rashin muhalli kana da lafiyarka ko mace fiye da daya Hisham kana da halin riketa to don Allah ka duba Hisham ba wai takura maka nake yi ba a,a so nake yi kai ma ace ko ka bar duniya to ka bar wanda za a gani ace naka ne wanda hakan ba zai sa a manta da kai ba a lokaci kankani". Dago kai yayi ya dube ta da damuwa kafin ya saki fara'a "Mami na! Shikenan naji in Allah ya yarda ba zan baki kunya ba a wannan lokacin kin san mi ma kawai ki nemo min matar aure kawai...". Wani kallo ta watsa masa. "Ban yarda ba ai bani zan zauna maka da matar ba don haka da kanka zaka zaɓo matar auren ka don haka maza tashi ka bani waje na baka lokaci kayi abin da ya dace". Kokarin kwanciya yake yi da dariya a fuskarsa ta dube shi. "Me zakayi kasan Allah ba yarda za ayi kana katoto da kai ka karasa ni maza tafi gidan ka kaje can ka kwanta ba wai ka zo nan ka isheni ba...wai shin sai yaushe zaka koma wajan aikin ka ne Hisham lokaci fa naja kuma nasan za su ne meka ban son abin da zai zo ana dana sani". "Na kusan komawa". Ya fadi yana mai mikewa domin a halin da yake yanzu sam bai so ayi masa maganar kin nan nasa sam ba ya gabansa wannan tashin hankalin da yake ciki ya ishe shi Sallama yayi wa Mahaifiyar tasa yayi tafiyarsa ita kanta ta lura da sauyin ɗan nata a lokaci guda sai dai fatan ta Allah yasa lafiya littafin Husnul Muslmin din ta dauƙa ta cigaba da dubawa. ******* Ya tsine fuska ta shiga yi ganin wanda yake kiranta sai da ta gama kare masa kallo kafun ta isa gareshi shikuwa sai faman yashe baki yake yi kamar wanda aka ce an bashi ita kyauta. Gaidashi tayi ba tare da nuna masa komai ba ta lura da Dr.Aqeel sosai yake son bata matsala a duk lamarinta sosai yake so yake haifar mata da tashin hankali lokaci da yawa yana zuwa amma sai yaji labarin Dr.Karami ya zo sannan zai fara mata zarya kamar wacce yake bi bashi a cikin satikan nan da Dr.Karami yayi Dr.Aqeel ya zo yafi a lissafa ta rasa mai yake nufi da haka sosai take hango kamar akwai wata manufa ta daban a zuciyarsa duk da ya nuna yana sonta din ta yarda amma ita halayensa ne ba su mata ba ya fiye zafin rai da mai da karamin abu babba ita kuma abin da ta ki jini a filin duniyarta zafin rai da sauri hassala... "Mariya ban san ta ya ya zan billo miki ba iyakar bakin kokarina nayi amma abin har yanzu dai ba canji ya kamata izuwa wannan lokaci kin bani matsaya domin ni dai da gaske nake ba karya nake miki ba ni ba karamin yaro bane da za ai ta kai kawo akan abin da bai fi shan ruwa wuya ba". In akwai abin da ta tsana a filin duniyar Dr.Aqeel to rashin iya kalamai sam magana yake yi kamar saukar markaɗe ga shi murya ba kadan ba gabadaya sai ta cika mata kai ba wai bata son sa bane a,a sosai take jin sa a ranta amma ba ta tunanin za ta iya zama dashi a inuwa daya. "Kice wani abu mana". Dago idanuwanta tayi ta dubeshi sosai Dr.Aqeel ba shi da makusa ko ta miskala zarratin amma bata san mai yasa zuciyarta har zuwa wannan lokaci ta kasa amanna dashi ba. Horn din da ya doki kunnuwansu ya sanya su gabadaya suka juya kallo daya Mariya tayi wa motar ta gane wanene wani irin bugawa taji gabanta yayi da karfi idanuwanta suka yo waje wani matsanancin tsoro taji ya ziyarce ta nan ta shiga kallon kallo tsakanin Dr.Aqeel da Motar Dr.Karami yanayin da Dr.Aqeel ya ganta aciki ya tabbatar masa da akwai wani abu domin shidai bai gane waye ma a cikin motar ba. Numfashi ta shiga ja a hankali ji take yi kamar ta kwasa da gudu sam bata so ace sun hadu da juna domin rabon dasu tsaya a tsakaninsu tun ranar da rigima ta kacame tsakanin Dr.Karami da Huzaif shikenan ta shiga wasan buya ko ya zo wajan ta sai ta san yarda tayi ta guje masa. "Zan shiga gida Sai anjima". Mariya ta fadi muryarta na rawa da sauri Dr.Aqeel ya dubeta cikin mamaki da tuhuma kafin ya motsa laɓɓansa yana cizansu. "Idan kika yi mani haka kina tunanin kinyi mani Adalci kenan Mariya me yasa wai baki son tsayawa ki fuskanci in da na dosa ne mai yasa kullu yau min in na zo wajanki baki taba bani lokacin ki...". Numfashi mai zafi ya fesar kafin ya sake kallon motar wacce har zuwa wannan lokacin ba alamun za a buɗe ta. "Ina son ki Mariya so mai tsanani kuma na san ke ma kina sona ko baki so ni dan komai kin so ni taimako...". Ware idanu tayi sosai tana duban Dr.Aqeel da take jin kalamansa na saukar mata kamar aradu aka jin in da ya dosa ya sanyata daga masa hannu. "Ban yi zaton haka daga gareka ba ban taba tsammanin zan ji haka daga gareka b Dr.Aqeel me kake son ce mani kana nufin ba saboda Allah ka taimaka mani ba ko me kana nufin dama akwai wata manufa a tsakanin taimakon da kayi mani". Lokaci guda idanuwansa sukayi ja bacin ranta ya bayyana sosai bakin ta na rawa ta sake dubansa kafin ta kau da kai. "Kenan ba don Allah kake so na ba kenan dama can kana da wata manufa ta daban a haka kake so na so ka a haka kake so mu zauna inuwa daya da kai a haka kake son ko mun zama ma'aurata ba zaka mance taimakon da kayi mani ko da laifi nayi maka goranta min zaka din ga yi kaico!". Ta fadi tana mai dauke kwallar da suka zubo mata a fuska a hankali ta shiga takawa tana barin wajan zuciyarta na wani zafi da raɗaɗi kirjinta take ji yana kartawa kwanyarta na hautsine wa. Gabanta ya sha cikin matsanancin tashin hankali idanuwansa sun kaɗa sunyi jajir. "Mariya me kike nufi da haka mai yasa zaki yi saurin yanke min hukunci akan abin da ba haka bane mai yasa kike kokarin fuskantata a hagunce na rantse miki da...". Da sauri ta daga masa hannu izuwa wannan lokacin idanuwanta sun kawo ruwa. "Ba abin da zaka ce mani Dr.Aqeel ba maganar da zaka sake fadamin na yarda na sani ni talaka ce wacce bata dashi wacce ubanta ya kawo su asibiti ya gudu ya bar su ba tare da komai ba...". Wani murmushi mai ciwo ta saki kafin ta dora da cewa. "kana da damar fada min komai ko mai kace ban ga laifin ka ba ni ce mai laifi mu muka zo wajan ka mu muka nemi taimako zaka iya fada mana komai amma ka sani a duniyar nan hanyoyin da Allah ya buɗe su da yawa suke domin wani ya zo ya nemi wani abu a wajan dan'uwansa ka sani komai yake faruwa dani da sauran iyayena ba mu muka daurawa kan mu ba ka sani ALKALAMIN ƘADDARA ne ya zana mana kuma ka sani duk wani dangin rai a duniyar nan ba yarda ƙadddararsa bata zuwa masa domin kuwa ba komai bane bawa ke nema ya samu Dr.Aqeel...". Runtse idanu tayi jin yarda zuciyarta ke zafi da raɗaɗi a duniyar nan in akwai abin da ta tsana shine ayi mata gori tana jin zafin hakan sosai a ranta shiyasa ta kullacin hakan a ranta cewa duk yarda zatayi rufawa kanta asiri zata yi domin ta lura a duniyar nan ba abin da yafi bakinciki da takaici shine ka nema wajan wani ya dizga ka ko kuma yayi maka bayan idonka ya zo yana zaginka ko yana goranta maka a duniyar nan ba abin da yafi kwanciyar hankali da gujewa wulakanci kamar DOGARO DA KAI. "Mariya don Allah kiyi hakuri wallahi tallahi ba haka nake nufi". "Don Allah Dr.Aqeel ka rabu dani in har ba so kake yi zuciya ta buga ba ka barni haka ka sani ban ga laifin ka ba don ka fadi haka maganar so kuma Dr.Aqeel ka sani ina son ka amma halayenka ne na tsana ba zan boye maka ba a yau na kara gasgata abin da zuciyata ta ɗade tana sanar dani bana tsammanin inuwa daya da kake kwadayin mi zauna a tare zai yuwu". Ta karashe tana mai kaucewa tana wucewa da sauri ya shiga kokarin shan gabanta wani kallo tayi masa hakan ya sanyashi tsayawa cak! Yana dubanta har ta karasa cikin sauri-sauri gudu-gudu. Zubewa ne kawai Dr.Aqeel bai yi ba a kasa domin zuciyarsa yake ji tana wani irin bugawa da sauri-sauri kamar zata faso kirji ta fito duniyar yaji tana juya masa bai san abin da ya kai shi yin wannan maganar ba bai san mai ya kai shi ba gashi yanzu bakin sa ya yanka masa wuya yankan da bai san ko zai warke ko ba zai warke ba yanayin da ya ga Mariya a ciki ba karamar kiɗima yayi ba a hankali ya fara taka kafafuwansa hannunsa rungume da kansa har isa wajan motarsa ya shiga kafun ya dago ya dubi Motar da tun dazu take tsaye ba tare da mai ita ya fito ba sosai yaji zuciyarsa tana azalzalarsa da ya tsaya ya ga kowa waye amma a halin da yake jin kansa a yanzu ba zai iya ba yana bukatar ya gansa a gida yana bukatar ya kebe kan sa waje daya domin yin tunani da samo mafita da za ta haifa masa da ɗa mai ido. A hankali yayi wa motar key kafun yayi ribas ya fizge ta da gudu ya bar unguwar zuciyarsa a jagule. Dr.Karami da zuciya ta kwasoshi tun dazu yana dannewa duk abin da ya wakana yana kallo ya dade yana zargin Dr.Aqeel akwai wani abu a tsakaninsa da Mariya bai gasgata ba sai yau da idanuwansa suka gane masa zuciyarsa yaji tana zafi da wani irin turiri sitiyarin motar ya buga tare da buɗe murfin motar ya fito sai faman huci yake yi kamar wani kumurci fuskarsa har ta canza launi saboda tsananin bacin rai ya shiga kai wa iska naushi kafin ya ja kakafuwansa zuwa cikin gidan da Sallama ya shiga ba kowa tsakar gida sai muryar Mu'azzam dake tashi cikin kuka sake sallamar yayi a lokacin Umma ta ansashi kafin ta bashi izini ya iso daga kofar dakin ya tsaya suka gaisa da Umma abin da bai saba yi ba yau yayi shi kansa sai da yaji wani bambara kwai wai namiji da suna Hajara ita kanta Umma sai da tayi mamaki amma ba ta nuna masa ba. "Mariya na ciki Umma ce ina son ganinta". Ya fadi murya a sake amma a zuciyarsa shi kadai ya san abin da yake ji Mariya dake dunkule waje guda tun dazu dama take jiran tsammani da sauri ta mike ta zauna tana rarraba idanu alamun rashin gaskiya sosai Umma ta shiga dubanta tana karantar yanayinta kafin ta wurga mata harara lokaci guda. "Tashi ki fice mani daga daki sakayya". Rau-rau tayi da idanu kamar zatayi kuka don yarda Umma tayi maganar ya tabbatar zargin da take yi yiwa Dr.Karami laifi tayi shi shi haifar da komai. "Tashi nace tun kafin na kwaɗe ki wallahi". Zabura tayi tana mike tana tura baki gaba har sai da ta ga Umma ta mike sannan tayi saurin ficewa daga cikin dakin bata same shi a tsakar gida ba hakan ya tabbatar mata yana waje a hankali ta fara takawa gabanta na faduwa a har ta isa cikin soron gida tana kokarin ficewa daga cikin sa sam bata lura da mutumin da ta wuce ba sai ji tayi ya kira sunanta a firgice ta waigo tana kokarin kwasa da gudu ya sha gabanta saura kadan ta fada jikinsa runtse idanu tayi jikinta ya shiga rawa sosai ta firgita da yanayin sa a hankali taji yayi gyarar murya. "Buɗe idanunki". Ya fadi ba yabo ba fallasa jin abin da yace ya sanyata buɗe idonta daya tana kallonsa harararta yayi da sauri ta mai da ta rufe kafin ta bude su gabadaya a firgice. "Ke kina tunanin wannan halin da kikeyi shine mafita a gareki ko a yarda kike a matsayinki na 'ya mace kina tunanin abin da kike yi mutuncin kine na lura Mariya gabadaya kin canza halayenki ba yarda na san ki a da ba wai har kece kullum baki wajan wannan saurayi ba ki wajan waccan kuna rigima a matsayinki na 'ya mace anya kuwa bana tunanin wacce ta san mutuncin kanta da darajar ta zata kasance a haka". Wata katangar tashin hankali taji ta rikito mata lokaci guda kanta ya shiga sarawa lokaci guda idanuwanta suka kawo kwalla ta shiga dubansa shikuwa nuna wa yayi ko a jikinsa amma can kasar zuciyarsa ji yake yi kamar ana hura masa wuta. "Duk mace mai daraja ba za ta taba kasancewa a haka ba Mariya kin bani mamaki kin canza mani ban yi tsammanin haka kika koma ba...ba ma wannan ba tun yaushe nake garin nan amma daidai da rana daya kin ki bani lokacin ki amma kin iya baiwa wanda zaku tsaya layi kuna rigima da su saboda ni bani da wata daraja a idanunki ban cancani ki tsaya dani ba shikenan na gode amma ki sani in har kikace haka za ki cigaba da rayuwa da samari kina da katon aiki a gabanki". Yana gama fadin haka ya fice daga cikin soron zuciyarsa na suya sosai yaji ba dadi a ransa da maganar da ya gaya mata amma haka kawai yake ji a zuciyar tasa ita kadai hanyarsa ta samu sauki duk da dai bai san ya zata dauki lamarin ba. Idanuwanta da suke zubda hawaye ta kure kofar da su tana jin wani tashin hankali mai girma yana wanzuwa gareta a hankali taji kafafuwanta na kokarin kasa daukarta zubewa tayi kan gwuiwowinta lokaci guda ta na sakin wani kuka mai ciwo da taba zuciya... *_KAMALA MINNA_**😘😘😘 [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA TALATIN DA TAKWAS. Ihu sukeyi gabadaya sun karaɗe wajan sai cukuikuye junansu sukeyi a waje daya cikin matsanancin tashin hankali kallo daya zakayi musu ka tabbatar suna cikin tsaka mai wuya gabadaya sun jeme sun yi baki kayan jikin su gabadaya sun gama fita hayyacin su wasun suma ko kallabi babu akan su. Janta yake yi yana faman dukanta da bakin bindiga itakuwa sai turjewa take yi tana janyon yan'uwanta suma sunan janta kallo daya zakayi mata ka gane tana cikin galabaitaccen yanayi idanuwanta gabadaya sun gama rufewa kawai fizgar ta yake yi har zuwa lokacin da ya fidda ita daga cikin wajan sai numfarfashi take yi can ciki tsakiyar rana yaja ta ya watsar da ita ga ranar ta kwala sosai kamar zata darkar da mutum. A hankali ta shiga kokarin buɗe idanuwanta jin zafin ranar na dukanta ta ko ina gashi ba wata wadatacciyar suttura bace a jikinta wando ne dogo sai riga ita ma doguwa iyakar gwuiwa da guntun hannu amma yanayin da kayan su ka koma sai ka ka rantsee yagaggune daga bola aka tsinto su kanta kuwa ba kallabi wasu hawaye suka zuba daga cikin rufaffun idanuwanta kafin ta tashi zaune tana faman cizon laɓɓanta. Wani irin murɗawa taji mararta tayi lokaci guda kamar yan hanjinta da mararta za su zazzage wata kara ta saki mai razanarwa kafin ta kai hannayentala duk biyun cikin galabaitaccen yanayi tana dafe wajan zubewa tayi gabadaya a kasa tashiga murkususu da shure-shure kamar kazar daka yanka take kokarin mutuwa cikin lokacin kankani ta fice daga hayyacinta ko motsi bata yi kafin can kuma jini ya balle ya shiga kwararowa ta kasanta mai dauke da gudaje-gudaje numfashi take ja jin komai na duniyar take kamar ba nata ba duniyar take ji tana canza mata da tashin hankali mai tsananin gaske zafin da take ji tun daga cikinta har zuwa mararta ya tabbatar mata da lokacin mutuwarta yayi sosai taji dumin da ke bin kafafuwanta hakan ya kara tsinkar mata da zuciya. Tsaye yake kanta yana kallon duk abin da ke faruwa amma ko motsi bai yi ba sai faman murmushi yake yi kafin ya juya ya dubi gabadayan alkaryar tasu sannan ya juya ya dubi sauran yan'uwan nata da ke kargame ko wacce da sakar a hannayenta da wuyanta sai faman zubda kwalla suke yi suna gunjin kuka hannu suke miko mata amma ina bata san ma a ina take ba lokacin da suka lura da abin da ke faruwa da ita ba su san lokacin da suka kara sautin kukansu ba cikin matsanancin yanayi. Bindigar da take hannunsa ya daga ya saita in da suke ji kake daram! ya sake nan take albushiri yayi fitar burgu ya sauka cikin wajan a saitin goshin daya daga cikin yan matan wani razanan nan ihu ta saki lokacin da kanta ya tarwatse kwanya ta watse duk ta bata yan uwanta kafin gangar jikinta ya zube kasa warwas. Ganin abin da yake faruwa ya ka sanya su cikin matsanancin rikici lokaci guda duk su rikice suka shiga kai kawo cikin wajan ko wacce hannunta akanta suna faman kankame junansu. Ihun da yake tashi ne a wajan yana ansa kuwwa ko ta isa ya sanya shi dago tambol din sa ya fito fuskarsa a murtuke kam! ya tsaya a tsaye yana faman bin filin wajan da kallo kafun ya sauke wajan yan matan da yake hangowa sun faman rusar ihu wata razananniya tsawa ya doka lokaci guda sautin tsawar ya karaɗe wajan ƙafin ya shiga takawa cikin matsanancin zafin rai idanuwansa da wani irin yanayi na tsananin rashin imani da tausayi idanuwansa na kan su sam bai lura da abin da yake gabansa ba sai da yaji yaci karo da mutum sannan ya tsaya yana duban wajan shame ya ganta ko alamun rai babu a jikinta da sauri ya daga kansa yana duban sa. "Ita kuma wannan fa?". Ya tambaya cikin yanayi na halin ko in kula kafun ya sake dubanta iya zuwa lokacin tana fidda numfashi a hankali hankali. "Shiga nayi na bukace ta shine ta saka min hakora a jiki". Ya fadi yana mai nannaɗe hannun rigarsa wani wawan cizo ne ya bayyana har fatar wajan ta dauke sosai. Ji kake kau ya dauke shi da mari kafi ya tsartar masa da yawu cikin tsananin dacin rai. "Mai ya hanaka rabata da filin duniyar nan tun da har zata yi maka taurin kai har haka". Yana gama fadin haka ya zaro wata karamar bindiga fisto ya saita ta lokaci guda ya sakar mata albushiri a kai shurawa daya tayi daga shi bata sake yin wani ba. "Wa ya fada maka ana jayayya da su ai duk wacce ta tsaya tsaiko a tsakanin ku kawai dauki ranta don ba su da wani amfani a gare mu". Ya fadi yana mai tsartawa gawan dake yashe tana zubda jini daga kanta yawu kafun ya juya cikin takun isa yana mai juya bindigar dake hannunsa har ya isa garesu tun da suka ga ya tunkara garesu suka shiga haɗewa waje daya suna cakume junansu numfashin su na fita da sauri-sauri cikin matsanancin faduwar gaba da tsoro mai tsanani jikin kofar ragar da aka rufe su da ita ya tsaya yana mai yawatawa da idanuwansa akan su kafin ya saki wata mahaukaciyar dariya mai matukar razana su ya shiga sakin albushirin bindiga wajan na ansa sautin fitar albushirun hakan ya kara firgitar da su kafin lokaci daya ya daka musu tsawa da ta sanya su yin shiru wasun su har da sakin fitsari. A hankali ya shiga kaucewa daga wajan yana faman cilla bindigar sama yana caɓewa har ya isa ga tambol din sa can nesa ya hangota tana ta faman kyalaye amai kamar zata amayar da kayan cikinta gabadaya ta gama galabaita numfashi kawai take saki cikin tsananin zafi da raɗaɗi gabadaya jikinta take ji ya canza komai nata jin sa take yi kamar ba nata ba a hankali ta shiga kokarin tashi amma jirin da taji yana dibarta ya sanyata komawa tayi zaman daɓaro idanuwanta sai faman shatatar da hawaye sukeyi gabadaya ta gama figewa ta rame kamar ba ita ba idanuwa duk sun zurma ga wani mahaukacin duhu da tayi kamar wacce ta shekara ba ta ga ruwa ba. A hankali ya tako ya iso gareta yana bin ta da kallo kafin ya dan ranƙwafa sosai ya tallabo haɓarta a dan razane ta dago kai ganin waye ya sanya ta buge hannunsa tana mai jan jikinta can nesa dashi zuciyarta na kara cushewa waje daya ta wani tarin bakinciki da takaici mai yawan gaske kallonsa take yi kallo na tsana da kiyayya fuskarta a murtuke sai faman huci take yi ji take kamar ta cafko shi ta shake shi ya mutu ko ta huta da wannan bakar izaya da ukuba da take ciki a filin duniyar nan bata san yarda zata kira wannan lamarin ba bai ta san mai zata ce da wannan al'amarin ba bata san ya zata kwatanta rayuwar kaskanci da take cika ba ta rashin yancin da mutunta kallon kanta take yi a wata banza wacce bata da saura galihu tun da ta fado filin duniyar azzalumin mara imani wanda ba abin da ya saka gaba sai daukar rai da bai ji bai gani ba. Murɗawar da cikinta yayi ne ya sanyata dafewa tana runtse idanu hadi da tura laɓɓanta duka cikin baki tana cizawa wata irin azaba ce taji tana kartar mata ciki da bayanta ji take yi kamar zata mutu don azaba da take ji hawaye suka shiga zuba wanda bata san ma suna zuba din ba kawai dumi take ji a sama kuncinta har zuwa kirjinta buɗe idanunta tayi ganin mutum tsaye akanta ya sanyata saurin matsawa tana watsa masa wani matsiyanci kallo mai cike da tsana da kiyayya mai girman gaske kafun ta shiga motsawa laɓɓanta suka shiga motsi hawaye sai faman ambali suke yi. "Ka sani wannan dariyar da kake yi akwai ranar da za ta zame maka kukan jini, karka yi tunanin wannan rashin imanin da kake nunawa ba ranar da zai zo karshe, karka yi tunanin cin zarafi da keta haddi da kake yi ba zai zo karshe ba, ka sani duniyar ma gabadaya sai ka barta kamar yarda kake zama SILAR AJALI ga wasu to ka tabbata yarda ko wani dan aike yake zuwa ya dawo to ka tabbata kai ma dan aiken ka yana nan dawowa kuma duk abin da kake aiken sa yayo kai ma sai ya zo ya yi akan ka". Numfashi taja tana jin yarda zuciyarta ke zafi da raɗaɗi da tashin hankali mai girman gaske. "Ka kashe mani iyaye na ka rabani da gari na ka keta min haddi ka zaja min UKU BALA'I bala'in da bai taba rabuwa dani ba ka ja zamanin bala'in da ba zai taba canzawa ya koma alheri da yake kamar da ba amma ka sani shi sharri dan aike ne wallahi". Mikewa ta shiga kokarin amma har lokacin jiri take ji wani fizga taji yayi mata ya watsar da ita kasa ya taka mata ruwan ciki da kafarsa mai dauke da wani kafcecen takalmi wani irin nishi ta saki hawaye suka zubo mata idanuwanta a runtse. "Ina so ace na mutu amma abu daya zan roki Allah ya banni nayi rayuwa har zuwa lokacin da zan ga karshen ka zan fi kowa farin ciki da murna a filin duniyar nan mutane da yawa na san za suyi farinciki duk da dai baya in ta tafi bata taba dawowa amma ina so ace mutane da ka saka wa ciwon rai ka saka su a BALA'I zan so ace sun ga karshenka Malik". Buɗe idanu tayi tana jin yarda zuciyarta take kara kekeshewa da rashin tsoronsa yinkurawa tayi zata tashi tana mai ture kafarsa daga ruwan cikin ta. Duban gawarwakin da ake kokarin dauka guda biyu na yan'uwanta tayi kafun ta dube shi fuskarta da murmushi mai ciwo. " 'Ya'ya Mata kayi wa haka ka sani komin daren dadewa wallahi sai hakkin su ya hanaka sukuni ba ganin ka na shiga rigar mutanan adalci kana nuna kai na Allah ne kana yaudarar mutane ta wannan hayar Uhmm...". Taja numfashi kafin ta girgiza kai. "Lokaci ne ba wanda yake hanyar sabawa Allah ya samu nasara komin lokacin kuwa da ya dauka yana cin nasara to akwai RANA DAYA tak! da zata zo ta rushe duk wannan nasarorin da yake zaton ya samu". Sosai ya har zuƙa jikinsa har rawa yake yi wani wawan cafka ya kai wa wuyanta nan ta shiga kakari idanuwanta sukayo waje sun kaɗa sunyi jajir wani huci ya shiga fetar wa kamar zai ci babu kafin yayi cilli da ita can gefe guda ta hadu da wani katon dutse ta gaban goshinta lokaci guda gun ya tsage ya shiga zubda jini sosai ta ji zafin wajan amma ba ta nuna hakan ba tashi tayi ta sanya hannunta ta na dauke jinin a hankali a ko ina na sashin jikin ta azaba take ji amma jarumar zuciyarta ta kiyin rauni. "Kisan kai da kakeyi ka dauka kuma aikin yi a filin duniyarka na rantse da Allah wata rana kai ma zaka mutu mutuwa kuwa ta wulakanci sai ka raina kan ka BAR GANIN ALLURA wallahi karfe ce bar ganin abin da kake yi kamar abun burgewa ne wallahi kai ma sai wannan hanyar ta zama silar barinka duniyar nan". Kallonta yake yi da wani irin yanayi na mamaki tun da yake bai taba gani mace mai taurin rai kamar ta ba tun da yake bai taba ganin an kwaso yan mata an kawo masa ya samu mai taurin rai haka ba har zata iya dubansa ta gaya masa magana son ranta ba tare da fargaba ko tsoro a fuskarta ba gyaɗa kai yayi kafin ya bar wajan yana faman dukan iska. Ita kuwa kuka ta saki mai taba zuciya da soya ruhi sosai ta durkushe hannayenta saman kanta ji take yi kamar ta hadi zuciya ta mutu ta bar wannan duniyar komai na cikin ta ba dadi sai yau ta kara tabbatar da cewa DUNIYA BA ALJANNA BACE ta tabbata bakomai cikin duniyar na sai ta shin hankali da rashin imani kaicon wannan rayuwa kaicon wannan zamani. ***** Numfashi take ajjewa kyar idanuwanta sun kaɗa sunyi jajir hannunta dafe da cikinta da take jin sa yana ta faman juyawa sosai ta shiga tashin hankali sosai tayi kuka kuka wanda har zuwa yau take yin sa kuma bata san ranar daina shi ba ta shiga kunci da ukuba da bala'i ta sani bata da wata dama da za ta sake zuwa mata ta dadin rayuwa ta sani ita kam rayuwarta ta gama karewa tunda ta fado hannun wadannan azzaluman mutanan maras imani da tausayi maras ganin darajar 'YA MACE ba su dauke ta a bakin komai ba 'Ya'ya Mata sun mai da su kamar Toilet din su na duk lokacin da suƙa bukata za su je su biya bukatar su ko hali ƙaƙa ne ba sa ganin darajar koma waye bata san wasu irin mutane ba ne su bata san wata alkibla suke bi ba har ga Allah zata iya cewa ba musulmai bane domin bata ganin su da suffar ni'imar musulci ba duk da dai suna ikirarin su din haka amma ita kam bata taba yarda ba. Nisawa ta sake yi Hawaye na kwaranyo daga idanuwanta kamar daga sama taji ana dauke mata su firgigit tayi ta dawo hayyacinta dubansa tayi kafun ta kau da kanta zuciyarta nayi mata zafi da raɗaɗi ji take yi kamar ta haɗiyi zuciya ta mutu da wannan bala'in da take ciki bata son ganinsa ko muryarsa bata son ji domin ganinsa kamar ganin bala'in rayuwa ne. Murmushi yayi yana sake kai hannunsa bisa kuncinta. "Ki yarda dani ki zauna dani mu rayu tare dake a filin duniyar nan ki yarda mu zama abu daya har gaban abada ni dake da abin da ke cikin ki". Wani irin zillo taji cikinta yayi kafun idanuwanta suyo waje sosai fargaba da tsoron da take ji a zuciyarta akan abun da take zargi shi ne ya tabbata tabbas haka ne maganar sa gaskiya ita kanta ta sani akwai abin da ke damunta sosai taji a jikinta komai ya canza sosai take jin motsi a cikin cikinta runtse idanuwa tayi duniyar taji tana juya mata kanta yana komawa kasa kafafuwanta na dawowa sama zuciyarta take ji tana yayyagewa muryarsa da bakaken kalamansa take ji suna ansa kuwwa akan ta da cikin kunnuwanta tartsatsi da rugugi take jin kwanyarta nayi. "Ban san ta zan sanar dake ba amma ki sani ina cikin yanayi na bukatarki a gareni ina so ki kasance dani har karshen numfashina sosai nake ji a zuciyata sosai da sosai nake jin zuciyata ta baki wani fili mai girma kina rayuwa ki sani ban taba kaunar wata mace ba ban ta taba son wata mace ba iyakata da mace na biya bukatuna da ita domin ni ban dauki mace a abun darajawa ko girmamawa ba amma akan ki ina ji a zuciyata ke ta daban ce". Numfashi ya ja mai tauri kafun ya kureta da idanuwansa masu firgitar da ita a ko wani lokaci. Bata san ya zata dauki wannan lamarin ba bata san a wani mizani zata ajje shi ba sosai take cikin wani mataki na rashin nasara a rayuwa sosai ta hango kaifaffan ALKALAMIN ƘADDARA ya daura tsininsa akan rayuwarta yana rubuta rubutun da take gani a matsayin ajalinta a duniyar nan rubutun da take ganin shine sanadin afkawar wannan rayuwar mai cike da tashin hankali da bakin ciki da ukuba sai yau ta kara tabbatar wa bata da sa'a ko daya a duniyar nan bata da sa'a matsayinta na 'ya mace bata da duk wasu ababe da mace zata yi alfahari da shi a duniyarta komai ya ruguje komai ya lalace wai ita ce yau dauke da juna biyu, juna biyun da ba ta hanyar aure ta same shi ba junan biyun da ya kasance ta same shi ta hanyar bala'i da masifa da jafa'i juna biyun da zata iya kiransa da shine ajalin rayuwarta. 'Yaa Zuljalali wal-Ikram'. Ta ambata a zuciyarta da take ji tana yayyagewa tana fadowa kirjinta da tashin hankali mai girma ga wani abu mai girman gaske da take jinsa tsakanin makoshinta da kirjinta ya tsaya cak!. Bata san me zata ce ba ita dai ta san rayuwarta ta kare rokon Allah take ya dauki ranta a filin duniyar nan rayuwar take ji gabadaya ta ishe ta bata son ta bata son komai na cikinta komai baki ne take gani bata burin sake maimaita WATA RAYUWA a duniyar nan burinta kawai numfashinta ya dauke a daidai wannan lokacin lokacin da take ji yafi komai zama bala'i a gareta. Hawaye suka cika gaba da zuba a idanuwanta shi kuwa sai hannu yake kai wa yana dauke mata su. "Ki ce wani abu ina son abin da yake cikin ki ina kaunarsa har dake kan ki ki yarda mu rayuwa a inuwa daya a tare har zuwa numfashin mu na karshe". Daga idanu tayi ta dubi sashin da yan uwanta suke gabadaya sun gama mutuwa yawancin su da sunyi musu fyaɗe suke kashe su wasu kuma in suka ki yarda da bukatarsu suke kashe su su jefa gawarwakin a ruwa tana kallo bata da damar hanawa a gabanta sun kamo mutane masu yawa suna yin yarda suke so da su tana kallon yarda ake nunawa yan uwanta mata zallar rashin imani da tausayi amma bata san yarda zata yi ba agabanta an kashe har bata san a dadi ba an sha daukar bindiga ana bata ko wuka da sunan ta kashe wani amma bata tunanin zuciyarta zata iya zama mara imani da tausayi har haka yan uwanta musulmai ake kashewa har ake bata damar ta kashe batare da laifin komai ba. Ruwan hawaye suka zuba mataa ta daga kai can nesa ta hango Baaba BG na kallonta tun da ta zo shi kadai ne mutumin da take kallo a mutum wanda ba irin su ba tana zaton shima kamar sato shi akayi kamar yarda suma aka sato su bata taba jin yayi magana ba bata taba jin ya buɗe baki ya furta kalma daya ba tausayinsa take ji mutum har mutum amma izayar da yake sha in da wahala na kisa da tuni ya mutu sosai ta fuskanci hakan bai son aikin da suke saka shi a lokuta da dama tana kallon yarda Malik yake basu umarnin aiwatar da wani aikin na mugunta amma shi sam ba yayi Malik lokuta da dama ya sha daura masa bindiga da sunan zai harbeshi amma sai ya fasa amma fa izaya ya na shanta ko yanzu da yake cikin razana tsaye sai faman gumi yake yi idanuwansa a sama yana kallon ranar da ta kyalla sosai idanuwansa sai faman zubda hawaye suke yi. Malik ya sanya shi akan idonta yake bashi wannan azabar don kawai yaki yin mubaya'a akan abin da ya saka shi... Karar albushirin da yaketo cikin dajin ne ya firgita su da sauri Malik ya mike yana kai kawo a tsakiyar wajan ita kuwa gabadaya ta firgice tashima ya gagare ta. Yaran Malik ne taga suna ketowa kan baburansu a guje kamar za su tashi sama gabadaya wajan ya kaure da karar albushiri sosai da sosai Malik ya nufi cikin Tamfol din sa cikin hanzari lokaci guda kuma ya fito jikinsa da wata riga baka wulik mai kauri ga wasu igiyoyi da suke barbaje a jikinta da hanzari ya keta hanyar da ya ga yaransa na shigowa gudu yake yi kamar zai tashi sama can nesa ya hango bataliyar sojoji sun tun karo wajen bindigogin sa kirar Ak47 ya ya cilla sama tare da caɓe su a hannayesa ya shiga gudu yana sakin wuta ko ta ina cikin dajin sai da yayi tafiya sosai yana zubda sojojin da suka tunkaro alkaryar tasa albushiri ko ta ina amma shi ko a jikinsa domin albushiri da ta fado kansa yake watsewa kasa batare da ya bula jikinsa ba sai dai rigarsa ta dau hayaki a daidai inda albushirin ya sauka sosai ya cigaba da tafiya yana kallon yarda ake ta kashe masa yara hakan ya kara harzuka shi matuka lokaci guda zuciyarsa ta shiga tururi fuskarsa na kara hautsinewa idanuwansa suka kaɗa sukayi jajir a daidai lokacin da ya tun kari inda yake hango bataliyar sojojin adaidai kuma lokacin albushirin bindigun nasa suka kare watsar da su yayi tare da yin wata uwar sufa ya yi kasa ya tura hannayenssa cikin ciyayin da ke wajan lokaci guda ya dago wata bingida mai saffurin mai jigida ya cilla sama kafin ya sake mai da hannunsa cikin ciyayin ya fizgo albushiri mai matukar tsayin gaske ya mike kan kafafuwansa da wani irin karfi gaske domin inda yayi tsalle ya dire sai da ciyayin wajan suka yi sama bindigarsa da ta shilla sama a daidai lokacin tayo kasa da hannu daya ya caɓe ta tare da zura mata albushirin nan ya shiga sakin wuta ko ta ina yana faman juyi kamar wanda yake amfani da wani maganakisun majajjawa. Abin da Malik bai sani ba shine sojojin sosai suka shirya domin kuwa ƙawayansu kayi wa dajin can bangaren alkaryar tashi tuni sojojin sun isa cikin ta suka shiga sakin wuta ga duk wani yaransa sosai yan matan suka firgita suka shiga ihu saboda sautin tashin albushiri da suke ta faman ji ko ta ina ba su tsinke da lamarin ba sai da suka mazaje na bajewa a kasa matattu Mubeena dake cikin Tamfol din Malik tana kai kawo hannuwanta saman kai sai faman du'a'i take yi da fatan Allah yasa masu CETON RAI ne a garesu. Wani albushiri ya ratso ta ciki wajan ya gogi kafatarta wani zafi ne mai cike da raɗaɗi ya ziyarce ta kwalla kara tayi da kafin gaske tare da zubewa a kasa ji take yi kamar hannu aka fizge daga jikinta zafin jinsa tayi a ko ina na sashin jikinta kararsa kuwa amsa kuwwa yayi cikin dodon kunnuwanta a hankali ta shiga jan numfashi da take jin sa kamar zai fice daga jikinta saboda tsabar azaba da raɗaɗi runtse idanuwa tayi a daidai lokacin aka banko tamfol din aka shigo sojoji ne guda biyu ko wane dauke da hula irin ta su ta sojoji hannayen su dauke da jibga jibgar bindigogi a resting din ta sukayi lokaci guda cikin cikin raɗaɗi ta buɗe idanuwanta ta kalle su lokaci guda ta mai da ta rufe tana jin suna surutunsu akan ta amma ko motsin arzuki bata iyayi ba daya daga cikin su ne ya lura da kafataɗarta da sauri yayi wa dan'uwansa alamu hakan ya tabbata masu alburushin ya same ta da sauri suka cinciɓe ta sukayo waje da ita gabadaya wajan ya zama fili sai gawarwaki dake baje can gefe kuma yan matan ne aka tare su waje guda sai faman rusar kuka suke yi gabadaya sun gama ficewa daga hayyacin su can suka nufa da Muneeba yan uwan naganinta da sauri su suka taso suka ansheta ganin halin da take ciki ya sanya su kara sautin kukan su kukan nasu ya farfado da ita daga sumar da tayi na wucin gadi a hankali ta shiga buɗe idanuwanta wanda hasken rana ya saito fuskarta komar da su tayi ta rufe kafin ta ciji laɓɓanta ta sake buɗe su sosai cikin karfin hali sosai ta shiga juya idanuwan nata tana kallon yarda sojoji sukayi wa wajan ƙawanya gabadaya numfashi taja mai tauri kafun ta dubi wanda suka riketa ganin yan uwanta ya sanya ta rushewa da wani irin kuka mai tsuma rai sosai da sosai jikinta har karkarwa yake nan suka sake buɗe babin kuka a tsakanin su sojojin sai bin su da kallo suke yi kafin su cigaba da shiga duk wani sashi na wajan. A bangaren Baaba BG kuwa lokacin da sojojin suka fara sakin alburushin ba zato ba tsammani yaji saukarsa a hannunsa na hagu da hanzari cikin wahalallen yanayi ya saki wani nishi kamar ransa zai fita ya saukar da kansa daga kallon ranar da yake yi wanda suka gama wahaluwa jijiyoyin kansa sun fito sun burɗun-burɗun da su kwayar idanuwansa sai faman zubda ruwa suke yi. Zubewa yayi a kasa yana kai hannun damarsa yana rike da hagun cikin wani irin yanayi mai matukar wahala sosai yaji kansa da duk jikinsa sun ansa da alburushin da ya fasa masa hannu runtse idanunsa yayi sosai kafun ya bude su dishi-dishi yake gani duban hannunsa yayi da yake ta faman zubda jini dafe wajan yayi sosai amma hakan bai hana jinin cigaba da zuba ba da hanzari ya shiga kokarin mikewa jiri na dibarsa sautin albushiri ne kawai yake ji ta ko ina zuciyarsa yaji ta kawo masa wani karfi mai girma gaske da hanzari ya tashi yana tangaɗi ko gani sosai bai yayi ya yanki daji yana jan jikin sa zafin raɗaɗi sai kara hauhawa yake yi tafiya ya yanka sosai sai yayi ta har kafafuwansa na kokarin kasa daukarsa amma zuciyarsa bata yi rauni ba karfi yake ji yana kara zuwa masa tun yana cijewa har ya fara gudu yana yankar daji numfashin sa na sama da kasa tafiya mai nisa yayi cikin wannan matsanancin halin har sai da sautin alburushirin dake tashi ya ragu yana jiyo sa daga can nesa bai ankara ba ya gashin gaban wani tafkeken kogi dake gudu cak! ya tsaya da tafiyar da yake yi yana mai da numfashi kafin ya zube kasa yana mai lumshe idanuwansa ko ina na jikinsa yake ji yana masa wani irin ansawa da ciwo mai tsanani buɗe idanuwansa yayi ya kalli hannun nasa da yake digar da jini ganin jinin ya fara bushewa hakan ya tabbatar masa ba karamar tafiya yayi ba ga hannunsa ya kumbura sosai ko ya ya taba shi zafi da radaɗi yake jin suna ansawa a jikinsa. A hankali ya tashi yana tangadi ya tunkari kogin sosai idanuwansa suna lumshewa bai san lokacin da ya isa bakin kogin ba har ya tsoma kafafuwansa kawai ji yayi ruwan ya fizgeshi da wani irin karfi ya antayashi ciki gudu kogin ya shiga yi dashi ba k'ank'autawa shi kansa bai sam ba a wani hali yake ba sosai ya mika dashi hanyar da kogin yake bi yana faman sama da kasa dashi. A bangaren su Malik kuwa abu ya kacame fada sosai ake yi ba abin da ke tashi sai sautin albushiri gawarwaki kawai zaka ke gani ko ta ina ta sojoji da ta alkaryar Malik wanda suka rage kalilan ne wuta kawai Malik yake tafiya yana yi idanuwansa a rufe ba zato ba tsammani yaji saukar wani katoton abu ya daki goshinsa ya cilla dashi can gefe ya bugu ta wata katuwar bishiya mai matukar girma kafin ya sake cilla wa wani wajan can daban ya fada cikin ciyayi har sai da ya shiga cikinta sosai da sosai runtse idanuwansa yayi kafun ya bude su sun kaɗa sun yi jajir yinkurin mikewa yayi amma ina bayansa yaji yayi wani irin amsawa kamar an karya bushesshen ice da sauri ya koma ya kwanta yana mai sakin numfashi ga wasu hawaye da suka shiga zubo masa a fuska ba kankautawa. hannayensa duk biyun ya cusa cikin ciyayin wajan ya damka kana jin sautin yardda suke rumurmushewa da yake sun bushe wani bakin ciki yaji ya tokare masa kirji ga wani abu mai girma ya tsaya masa a makoshi da k'yar yake jan numfashi komai. A karo na biyu ya sake buɗe idanuwansa jin motsi ta ko ina sojoji akansa sun yi masa ƙawanya sosai da sosai ko wannan su hannunsa dauke da bindiga sun saita shi wani takaici ne ya sake kume shi ya kurma wani irin razanan nan ihu da ya ansa sauti sosai cikin dajin... *_KAMALA MINNA_*😘😘😘😘 [8/26, 7:29 PM] 80k: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA TALATIN DA TARA. Juyi kawai take yi zuciyarta na zafi da wani irin raɗaɗi mai girman gaske sosai take jin komai ya sauya mata sosai take jin duniyar da abin da ke cikinta sun zame mata kunci da ukuba komai take kallo a mara dadi zuciyarta da ruhinta suna wani mataki na tashin hankali ba abin da take tunawa sai kalaman Dr.Karami sosai suka taba mata zuciya da ilahirin jikinta bata taba zato ko tsammani ba ko a mafarkinta bata taba zaton Dr.Karami ya dube ta ya na gaya mata magana son ransa har haka ba ko da yake bata ga laifinsa ba har da ita da ta tsaya tana kai kawo akan sa ashe duk kulawa da yake nuna mata a zahiri ba haka bane zuciyarsa sam bata tare da ita. Wasu hawaye ne masu zafi suka zubo mata da saurin ta kai hannunta ta shafe su don bata so Umma ta lura da halin da take ciki yau kusan sati uku kenan amma ta kasa manta kalaman Dr.Karami sai faman kuwwa suke yi mata akai da kunnuwa ta rasa mai yake yi mata dadi a filin duniyar nan bata san abin da ke kokarin faruwa da ita ba ta ji zafin kalamansa amma kuma zuciyarta taki bashi laifi taki yarda da laifin da take dorasa masa bata ma san mai haka yake nufi ba tun da abin nan ya faru ta kasa sukuni tunanin Dr.Karami ya sha mata kai ko barci take yi shine dai take tadda cikin barcin nata. Mikewa tayi daga shingiɗen da take ta shiga safa da marwa a cikin dakin domin samowa kanta mafita sosai take jin ciwo mai girma a zuciyarta sosai take jin gangar jikinta na kawo mata bakutan wani yanayi mai girman gaske wanda ta rasa yarda zata kwatantashi sosai Dr.Karami yashiga yin tasiri akanta da kalamansa da suka hanata sukuni. Bata san mutum na tsaye ba kuma za ta iya cewa ga lokacin da ya shigo yana jima yana dubanta da yanayin ta kafun ya motsa laɓɓansa cikin wani irin yanayai. "Ya jikin naki?". A firgice ta juya jikinta har rawa yake yi jin sautin muryarsa lokaci guda ta dube shi da idanuwanta da suka kaɗa sosai shima ita yake kallo da wani irin yanayi mai girman gaske kallon kallo suka shiga yi a tsakaninsu da wani yanayi wanda suka kan su ba su san haka na faruwa a garesu ba sun jima a wannan halin kafun Dr.Karami ya kau da idanuwansa jin zuciyarsa na bijiro masa da wasu lamura da ya tabbata ba za su haifa masa da ɗa mai ido ba numfashi yaja mai tauri yana jin yarda zuciyarsa ke buɗewa da wani yanayi akan Mariya sosai yake jin ko wani sashi na jikinsa na ansa amon tausayawa da yanayin da ya ganta a ciki bai yi tsammanin lamarin ya kai har haka ba nisawa ya kuma yi yana fesar da wani zazzafar huci kafin ya dago idanuwansa da suke lumshewa kamar mai jin barci. "Uhmm jiya munyi waya da Umma take sanar dani wai baki da lafiya". Ya fadi yana mai yawatawa idanuwansa akan fuskarta da wani irin yanayi mai taba zuciya yatsine fuska ta shiga yi tana kau da kanta gefe kafun ta motsa laɓɓanta kamar wacce akayi wa dole. "Ni ba abin dake damu na". Ta fadi da yanayin fushi a muryarta murmushi yayi kafun ya taka ya karasa shiga cikin dakin hannayensa sarƙe a kirjinsa ya zuba mata idanuwansa sosai yana mata kallon tuhuma kallon da take ji har cikin jikinta yake shiga ji take yi kamar zata narke ta watse a wajan. "Kin fiye gardama wallahi kenan Umma karya take yi miki ko? Sau nawa ina kiran wayar ina cewa a baki amma bakya ansa na sani ba wai rashin lafiyar ta hanaki ansar kirana ba fushi kike yi dani ko akan abin da na san na fada miki gaskiya ko". Da sauri ta dube shi idanuwanta a warware kafin ta tura baki gaba. "Fushi fa kace kai din ne zan yi fushi da kai akan wani dalili saboda ni kuma gani wahallaliya ko bani da aikin yi". Tun da ta fara magana yake kallon ta da mamaki mai girma a ransa dubanta yake yi har ta dire kafun ya ja wani numfashi yana jin yarsa zuciyarsa ke wani irin juyawa a mataki na wahala runtse idanu yayi kafun ya sake buɗe su kalaman nata yake jin su kamar saukar ruwan zafi a dukkan sassan jikinsa takawa ya shiga yi yana isa gabanta ganin haka da tayi taja baya da sauri shikuwa bai bar takawa gabanta ba har sai da ya kusan mannuwa da jikinta sannan ya tsaya. "Me kika ce maimaita ban ji ba". Ya fadi yana mai karkaɗe kunnuwansa fuskarsa a daure tamau hakan ya fadar mata da gaba don ta tabbata maganarta ta bata masa rai sosai don ga fuskarsa nan ta nuna. "Maimaita mana ina jinki". Ya sake fadi yana watsa mata wani kallo da ya razana mata zuciya da sauri tayi baya har tana kokarin faduwa kasa. "Ni kike fadawa haka ko Mariya Good kin kyauta". Yana fadin haka ya juya yana kokarin fita juyowa yayi ya dubeta sosai. "Dr.Aqeel da Huzaif ba zan hanaki tsayuwa da su ba don na lura su ne kika mai da abokan zama har kuna SA'INSA amma ki sani ko samarinki ne ko auren su zakiyi dole ki fidda daya domin kuwa maza biyu ba auren su ake yi ba gabadaya kisan da wannan". Yana gama fadin haka ya dage labulan ya fice daga cikin dakin. Sosai ta ware idanu waje jin maganar da yake fadi mata sosai taji zuciyarta ta tabu ta rasa mai Dr.Karami yake nufi da haka ta rasa mai ya mai da ita da yake fadi mata irin wadannan kalaman wayace masa son su take yi wa yace masa samarinta ne har yake gaya mata magana har haka. Dafe kanta tayi da take jin yana barazanar tarwatsewa ta runtse idanu tayi tana jin wani zuki da raɗaɗi na taso mata tun daga kasar ruhinta yana direwa a dukkan jikinta sosai taji duniyar na juya mata komai take ji yana kara hargitsewa sosai kalaman Dr.Karami suke taba ta don ta lura kallon wata mace daban yake yi mata mai wani hali na daban... "Ke Mariya wai shin meke damun ki ne? na rasa gane kan ki gabadaya kin daurawa kan ki wani bakin hali da ZURFIN CIKI wanda ban san ki dashi ba". Maganar Umma ce ta katse mata dogon tunani da ta afka da firgice ta juyo tana duban Umma da ke tsaye bakin kofa tana watsa mata wani irin kallo. "Na gaji nagaji da halin ki Mariya haba mana ke kenan kullu yau min ki hana kan ki sukuni ki hana wasu kuma haba mana ai wannan shiga Hakki ne an tambayeki me ke damun ki kin ki fadi to ya kike so kiyi yanzu shima Hisham din ya zo daga yanayin da ya fita na san ke ce kika bata masa rai ko shikenan ki cigaba da yi abin da ranki ke so karki daina kin jiko". Tana gama fadin haka ta juya ta fice daga cikin daki ranta a matukar bace. Mariya da tayi mutuwar tsaye ta shiga duban kofar kanta na kara rikicewa da sarawa sosai taji komai ya sake kwance mata wani abu mai nauyi take ji ya zo kirjinta ya zauna sosai kwallar da take makalewa taji sun zoba mata akan kuncita kafafuwanta taji suna kokarin kasa daukarta da sauri tayi kasa ta zube wani kuka taji ya zo mata ba zato ba tsammani kanta ta tura cikin cinyoyinta jikin har k'yarma yake yi hawaye suka balle mata kamar an buɗe famfo ita kam bata san yarda zata cakuɗa wannan lamarin ba komai ya kulle na kanta sosai take jin tashin hankalin na daɗuwa a filin duniyarta. ******** A hargitse ta fado cikin gidan bayan mai gadi ya buɗe mata Get din sam ba ta lura da wanda yake gabanta ba sai da taji ta daki mutum tayi taga taga kamar zata fadi da sauri ya riko mata hannu idanuwanta a rufe don ta sadakar ta je kasa jin an riketa ne ya sanyata saurin buɗe idanuwanta ta sauke su a cikin nasa da suke zube akan ta. "Tareeq". Ta furta tana mai zare idanuwanta sosai kafun tayi hanzari fizge hannunta taja da baya. "Yi hakuri don Allah wallahi ban gan ka bane...". Hannu ya daga mata idanuwansa na kan wayarsa ba tare da yayi mata magana ba ya rabata ya wuce abin sa wani takaici ya kule ita kam bata san wani irin hali wannan mutumin gareshi ba na shariya da kyaliya tun da ta fara ganinsa a hakan dai yake jiya iyau ko muryarsa bata taba ji ba sosai hakan ke taba mata rai ta ki jinin mutum mai irin wannan hali shiyasa Dr.Karam... Shiru tayi da sauri jin tunaninta na kokarin canza jaha da sauri ta figi kafarta tayi cikin gidan. Abin da bata sani ba shi Tareeq ko da ya tafi makalewa yayi yana kallon ta da wani yanayi wanda shi kadai ya barwa ransa tun ranar da ya fara ganin Mariya yaji gabadaya ta tafi da imaninsa amma ya rasa ya zai yi kuma gani yake yi kamar da raini ace k'awar kanwasa yake bibiya shiyasa ke ta faman tsare gida shi ala dole girma ne nan yake dauka bayan kuma zuciyarsa ta jima a wani fanni na rashin wannan girman don tuni ta yasar dashi akan abin da tajima tana so. Numfashi ya ja yana fesarwa kafin ya fice daga cikin gidan. Ko da tashiga cikin falon ba kowa sai karar Tv kawai dake tashi numfashi taja kafun ta ja kafa da sauri ta haye saman bangaren Baseera kofar a buɗe ta same ta don haka da sauri ta tura ta shige kwance ta hango Baseera tayi ɗai-ɗai saman gado sai faman zabga murmushi take yi kamar wacce aka zunduma gidan aljanna kunnan ta dauke da waya alamun wayar da takeyi mai muhimmanci ce turjiya Mariya tayi ta harɗe hannayenta a kirjinta ta zuba mata ido cike da mamaki kafun taja kafarta da sauri ta isa gareta duka ta daga mata ganin yarda ta saki jikinta har rigar ta na tattarewa cinyoyinta sun bayyana a firgice ta tashi ta zunduma ihu ta cillar da wayar can gefe idanuwa warwaje Mariya da ke tsaye bata san lokacin da ta kwashe da dariya ba tana dubanta ita kuwa Baseera nar-nar tayi da idanu kamar zata yi kuka kafin ta yi hanzari sankowa daga gadon ta cakumi wuyar Mariya. "Idan kina da mutunci in nitse wallahi baki da mutunci sam!". Ta tureta can gefe tayi tana susar cinya inda Mariya ta dake ta. "Ai ke za a kira haka wannan ai rashin hankali ne kina waya har baki san kayan suna kokarin bayyana jikinki ba yanzu in da wani ya shigo ya ganki a haka fa me kike tsammani". Gefen gado ta koma ta zauna tana faman turo baki gaba tana rarraba idanu in da zata ga wayarta can gefen gado da hango da sauri ta rarrafa ta dauko kafin ta shiga kaɗa idanuwa. "Yo ba dole na fada cakwalkwalin nishadi ba ni da mai kaunata ne fa rabin raina sakata zuciyata jinin jikina...". "Ke dalla jaye ki bani waje mara kunya kawai". Baseera ta kwashe da dariya tana tafa hannaye. "Ba maganar rashin kunya akan me zan cuci akai na haka kawai ai dole na tattali kayana ke kin san kuwa yarda nake son wannan gayen kuwa ya hadu iya haduwa ko ta ina ke dai kawai bari sai kin ga Fine Bobo dina sai kin kusan mutuwa ke dai yi ta zama a haka ba ki ga tsuntsu baki ga tarko yan maza sai gwara kan ki suke yi kin kasa fahimtar komai ki kasa sanin komai AKAN SO wallahi tun wuri ki koyi soyayya malama ki ji yarda ake fadawa cakwalkwalin nishadi wayyo Allah sahibi na mai sona ina son ka". Wani tukukin bakin ciki ya turnuke Mariya ganin yarda Baseera ke wani narkewa tana bin lafiyar gado sai wani lumshe idanu take yi mamaki ne ya cikata har yaushe Baseera ta koyi soyayya har haka ita bata sani ba ko WUKA A MAKOSHI zata gani bazata iya cewa ta taba ganin Baseera da saurayi ba amma yau RANA DAYA wai soyayya take yi ta gani kashe har tana koranta mata tsaki taja kamar harshenta zai tsinke kafun ta mike tana hararar Baseera kamar idanuwanta za su zubo kasa. "Wayyo Allah My Dr.Hisham". Baseera ta fadi tana kara rungume fulo sosai sai narkar da idanu take yi. Sunan da ta kira ne ya sanya Mariya firgita tana dubanta bata san lokaci da ta isa bakin gadon bata zauna idanuwanta a warwaje. "Me kika ce Baseera wani suna naji kin kira". Sake narkewa tayi kafun ta mike zauna tana sakin wani lallausar murmushi. "Abin da kunnuwanki suka jiye miki mana masoyina nakira ko saɓo nayi ne nayi saurin tuba". Girgiza kai Mariya ta shiga yi cikin wani irin yanayi sunan da Baseera ta ambata ba karamin tayar mata da hankali yayi ba in har ba kuskure tayi ba kamar sunan Dr.Karam ne takira ko da sunan masoyin ta anya kuwa ko dai ba shi bane ai masu sunan da yawa a filin duniyar nan zuciyarta taki gasgata haka ta fi yarda da Dr.Karami ne masoyin Baseera wani irin bugu taji kirjinta yayi da sauri ta dafe tana faman jan numfashi kadan-kadan duban Baseera tayi wacce sai faman danne-danne takeyi a waya fuskarta da murmushi. "Cikin raina na sanyoka ka bani guri nima in shigo naka". Baseera ta fadi tana rungume wayar a kirjinta idanuwanta a lumshe kafun ta buɗe su akan Mariya da tayi fakare tana dubanta kirjinta sai faman lugudan bugu yake yi. Tsaki taja na karo ba a dadi kafun ta ja numfashi. "Wai meke damun ki ne haka wajan ki fa na zo amma kin tsaya kina raina min hankali in ba zaki kulani ba malama na tashi na san in da dare yayi mani". Ta karashe a hassale kamar zata kife Baseera da mari. "Haba my Besty ina ni ina raina miki hankali kawai dai kisan in mutum ya tsunduma cikin kogin love din nan ne abun ne ba sauki walla...". Tun kafun ta karasa Mariya ta mike kan kafafuwanta sai faman huci take yi kamar zata hadiye Baseera wani kallo tayi mata kafun ta ja kafa da sauri tana kokarin barin dakin ganin haka da Baseera tayi da sauri ta mike ta riko hannunta sosai. "Yi hakuri mana mai yayi zafi shi ba wuta ba haba mana Besty bai kamata kiyi mani haka ba zo muje ki gaya min abin da ke faruwa na lura da yanayin ki kina cikin damuwa sosai". Fizge hannunta tayi rai bace kafun ta dubi Baseera. "Ni ki rabu dani kawai tafiya zan yi...". Ware idanu tayi sosai ta sake riko hannunta murya a kasa cikin rarrashi. "Zo muje na baki labari kin ji san nan ki sanar dani abin da ke damun ki a duniyar nan besty baki da wata k'awa wacce tafi ni nima kuma bani da wata k'awa wacce ta fiki mu rufe MATSALOLINMU a tsakaninmu tare da samun mafita ba tare da kowa yaji ba don Alalh zo muje mana". A hankali taja hannunta ta kaita bakin gado ta zaunar kafin taje ta dauko mata ruwa mai rangwamin sanyi tare da lemon Exotic ta dire mata a gabatan amma Mariya ko kallo ba su isheta ba halin da take ciki a yanzu ji take yi kamar zuciyarta zata kama da wuta don bala'in da take ji a ranta komai take ji ya rikice mata kwanyarta ta tsaya cak! da aiki. "Ban san me zance miki ba Mariya akan wannan lamarin amma ba karamin taba min zuciya yake yi ba na rasa yarda zan kama domin samo mafita na rasa gane kan ki kin ki sakin jiki ki fayyace abin da ke damun ki sannan in aka ce ga abin da ke damun ki baki daukar haka ne sai ki nuna kin amincewarki zuciyarki na wahalar dake sosai da sosai akan abin da kika san gaskiya amma kin ki amsa". Baseera ta fadi fuskar da yanayi na tausayi kafun ta mike kan kafafuwanta da wani irin yanayi na sanyi jiki taku tayi daya biyu kafun ta juya ta dubi Mariya wacce zuciyarta gabadaya ta gama sakin wannan layin da Baseera ta dauko maganar soyayyar Baseera ce yake kai kawo akan sa wanda ke fadar mata da gaba baka dan ba tagumi tayi hannu bibbiyu idanuwanta cikin yanayi na tsananin damuwa. "Kullum abu cigaba yake yi na rasa in da kika sa gaba na lura kina jin dadin rayuwa a haka ne shiyasa sam baki damu da kan ki ba baki damu da matsalar da kike ciki ba ZURFIN CIKI da kike yi wallahi ba zai kai ki ko ina ba zuciyarki ne zata haifar miki da matsala tun da kin kasa gasgata abin da take zuwa miki dashi". "Baseera wai da gaske soyayya kike yi?". Mariya ta fadi cikin yanayi na faduwar gaba da ansar da Baseera zata bata akan hakan kallon sosai Baseera ta shiga yi mata jin ta saki layin da ta dauko mata na matsalar ta ta dauko wani na daban murmushi tayi kafun ta juya idanuwanta sosai. "meye abin yi mani wannan tambayar Mariya ya za ayi muna wata magana ki na dauko wata kum...". "Tambayarki nayi ansa nake bukata kawai". Mariya ta tare ta a hassale kamar zata fizgota daga tsayen da take. Juyawa tayi kamar zata fice daga cikin dakin kafun ta sake juyo ta koma cikin dakin sosai tana bin Mariya da kallo murmushi dauke a fuskarta. "Bana tunanin wani mugun abu nake yi bana tunani saɓo nayi don na fara soyayya lokaci nane yayi na kai matsayin ace ina da saurayi kamar yarda ake bukatar ko wata 'ya mace ta kasance da saurayi in har lokacin ta yayi...ko da yake naga kamar mamaki kike yi ko Mariya amma ban san dalilin ba". Wani irin zillo taji zuciyarta tayi gabanta ya buga da karfi a hankali ta shiga rintse idanuwanta tana tura laɓɓanta cikin bakinta da wani irin yanayi mai girman gaske a zuciya mai tattare da kunci buɗe su tayi akan Baseera da take kai kawo a tsakiyar dakin fuskarta da annuri na farinciki so take yi ta tambayeta da wa take soyayya amma tana tsoron ansar da zata bata domin kuwa sosai gabanta ke dokawa da tashin hankali mai girman gaske akan Baseera sosai zuciyarta take gasgata zarginta sosai take jin gangar jikinta na amanna da lamarin mikewa tayi kan kafafuwanta da yanayin na karfin hali domin har wani jiri-jiri take gani taku tayi daya kafun ta sauke kanta kasa tana ambaton sunan Allah ya tsareta da mugun ji. "Uhmm naji kamar kin ce Dr.Hisham ko". Ta fadi dak'yar kamar wacce zata fashe da kuka gabanta na dokawa da tashin hankali. "Yarda kika ji haka lamarin yake ba kokwanto kike yi ba shine mai kauna ta din". Baseera ta fadi a iyakacin gaskiyarta ba alamun wasa wani irin zubewa Mariya tayi bakin gado numfashinta na fita a hankali-hankali kamar wacce tayi gudun CETON RAI idanuwanta ta runtse da karfin tsiya ji take yi kamar ba ita ba komai take ji na jikinta yana narkewa da wani irin tashin hankali wanda tun da take bata taba jin zuciyarta ta kawo mata haka ba jikinta har ɓari yake yi ta buɗe idanuwan nata da suka fara kaɗawa cikin karfin hali ta shiga saita kanta tana kalato murmushi mai sanya ciwo a zuciya mikewa tayi kan kafafuwanta tana kallon Baseera da ta zuba mata idanu da wani irin yanayi kafun tace. "ba laifin kaddara a lamarin nan naki Mariya har da laifin ki komai ke faruwa ya kamata ki sassautawa kan k...". Daga mata hannu tayi cikin karfin hali ji take yi kamar zuciyarta zata tarwatse jikinta take ji yana wata irin k'yarma kamar wacce aka jonawa wutar nepa. "Wai kina nufin Dr.Karami dai Baseera". Ware idanu Baseera tayi sosai lokaci guda yanayin ta ya sauya kafun ta motsa laɓɓanta idanuwanta aƙan Mariya tana karantar yanayin da take ciki. "Kin san dai a filin duniyar nan tamu ba wani Dr.Hisham bayan Karami ko...". Ai bata kai aya ba tuni Mariya ta fice daga cikin dakin cike da tashin hankali mai tsananin girma da kokarin yayyaga zuciya da jiki baki daya kafafuwan kawai take dorawa a duk in da taji sun sauka har ta isa cikin falon ba kowa hakan ya sanyata ficewa da sauri hannayenta saman kirjinta idanuwanta sai lumshewa suke yi a hankali kamar wacce ke jin matsanancin barci haka ta isa bakin Get ko maigadi batayi wa magana ba ta buɗe kofar ta fice cikin hanzari hanya ta dauka sosai tana tafiya idanuwanta da wasu zafafan hawaye da suke ambaliya so take yi ta karya abin da kunnuwanta suka jiye mata so take yi ta karyata zuwanta gidan su Baseera a zahiran ce so take yi ta karyata kanta da kan ta ba taji wannan furucin ba so take yi ace ma a tashi duniyar baki daya ba tare da tabbatuwar wannan lamarin ba baza ta iya dauka ba zuciyarta baza ta iya daukar wannan lamarin ba ina! ba zata iya ba so take yi a tashi duniya so take yi a ce tashin alkiyama ne so take yi komai ya zama tarihi kamar ba ayi shi ba. Wasu hawaye masu kokarin dauke fatar fuska suka sake balle mata zuciyarta take ji na kara kamawa da wuta ji take yi kamar narkewa take yi ji take yi kamar ba ita bace ji take yi kamar ba a halicce ta ba a filin duniyar nan. Sam bata lura ta kai bakin titi ba har ta hau tsakiyarsa ihun mutane da Horn din motoci ya fargar da ita cikin razana zare idanu tayi waje ganin irin Go-Slow din da ta hada mutane wasu na ganin kamar bata da hankali wasu kam danna mata ashar kawai suke yi gaɓadaya ta firgice ta rasa ina zatayi hayaniyar mutane ya kara razana mata kwakwalwa hannu ta daura akai tana kokarin kurma ihu taji an ja hannunta anyi gefe da ita runtse idanu tayi jin wani irin Shock da ya ansa duk kan sassan jikinta da sauri ta buɗe idanuwanta buɗe baki tayi tana kokarin kurma ihu ganin wanda ke rike da ita da sauri ya sanya dan yatsarsa akan laɓɓansa fuskarsa ba wasa alamun tayi shiru tsit tayi amma har lokacin fuskarta da tashin hankali jikinta sai k'yarma yake yi fizge hannunta tayi tana faman ja da baya shi kuwa bin ta yake yi da kallo cikin tsananin mamaki da tu'ajibi hannayensa harɗe a kirjinsa ganin dai tana kokarin komawa kan titin da sauri ya fizgota ya ja ta kamar zata kifa can inda yayi parking din motarsa ya isa ya buɗe gidan gaba ya bata umarnin shiga amma taki sai faman tirjewa take yi tana faman wurga masa mugun kallo take yi kamar idanuwanta za su fado kasa. Shi kan sa sai da ya ji gabansa ya fadi da kallon da Mariya take yi masa kallon da ya tabbatar akwai abin da yasa take yi masa shi kallo ne na tuhuma kallo ne kuma na ka yaudare ni kallo na kayi mani ba daidai ba. "Please Mariya shiga daga ciki mana...". Fizge kanta tayi tana kokarin raɓashi ta wuce batare da ta shiga motar ba amma ganin irin tsayuwar da yayi babu wasa ga wani girma taga yayi mata da kwarjini wani irin bugu taji gabanta yayi lokacin da taga rinannun idanuwansa ta kalle shi kallon da taga yana jifanta dashi da yanayin da taga kwayar idanuwansa na canzawa gabadaya ya firgita ta da sauri tayi kasa da kai. "Muje nace". Ya fadi da wata murya wacce ba wasa a cikinta dubansa ta sake yi cikin nuna son yin gardama amma yarda taga ya tsare gida sosai ya sanya jikinta mutuwa murus ta tokare bakin kofar ita bata shiga ba ita kuma ba ta wuce ba. "Yaa Allah! Mariya kina da matsala sosai a rayuwarki kin fiye taurin kai". Ya fadi yana dafe kansa da wani yanayi na damuwa kafun ya sake dubanta wacce ita ma a lokacin ta dago kanta ta watsa masa kallo. "Nifa ba zan shiga ba kawai ka rabu dani kayi tafiyarka ba abin da ya dame ka dani ba abin da ya dame ka da yanayin da nake ciki don haka Leavea Alone Please". Da mamaki yake dubanta jin maganar da take fadi wanda suka kusan tarwatsa masa kai amma sai ya maze cikin tsare gida sosai ya nuna rashin wasa. "Kisan Allah ki shiga motar nan tun kafin raina ya baci don na lura sai na nuna miki kala irin taki sannan zamu zauna lafiya dake ban san abin da yake hawa miki kai ba ban san mai yasa gabadaya kike kokarin sanya kan ki cikin matsala har haka b...". "Wannan ba damuwarka bace kawai ka rabu dani nayi tafiya...". Ai ba ta kai ga dire zancenta ta ji ta saman set din motar baje numfashin da take ji na sauka akan fuskarta ne ya sanyata saurin dubansa kallonsa tayi shima ita yake kallo da matsanancin bacin rai sai faman huci yake yi tana jin yarda zuciyarsa ke bugawa da sauri-sauri sosai take kallonsa ta kasa dauke idon ta kamar yarda shi yake kallonta da wani yanayi wanda ya shiga haifar mata da kasala mai tsanani gabadaya taji duk wani tashin hankali da take ji da bacin rai game dashi yana kaucewa a hankali wasu kibiyoyi take hangowa suna fitowa daga cikin idanuwansa suna sauka ana ta sosai taken jin zuciyarta na buɗewa da wani lamari mai giraman gaske kallon Dr.Karami take yi kamar bashi ba kallonsa take yi a wani mutum mai kwarjini da haiba gami da cikar zati wani kallo take jifansa dashi kamar tun da take bata taba ganin mai kyau da k'yan kallo kamar sa ba. Hure mata idanu da yayi ne ya dawo da ita hayyacinta ba tare da yace da ita komai ba ya juya dayan barin na zaman direba ya shiga yayi wa motar ki har zuwa lokacin fuskar tashi ba alamun wasa sai ma kara tsare gida da yake yi ita kuwa gabadaya ta gama narkewa sai faman juyi take yi ta kasa zama sosai a kujerar da take duk yana kallon yanayin ta har ya yiwa motar Key ya cillata saman titi yana mai kara sautin wakar 'BECAUSE OF YOU' ta Amanda Mena dake tashi a cikin motar... *_KAMALA MINNA_*😘😘😘😘 [9/3, 7:45 PM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA ARBA'IN. Sosai take kai kawo cikin dakin gabadaya ta kasa zaune ta kasa tsaye tunda Dr.Karami ya zo ya ajje ta a kofar gida ya juya ya tafi ba tare da ya dubeta ba balle yace da ita k'ala hakan ba karamin taba mata zuciya yayi ba duk da tana jin wani iri a game dashi na bacin rai duk da ta san dai fushin da take yi dashi ba ta san ya yake ba amma ta tabbata halin ko in kula da ya nuna mata a yau yayi matukar sanyata cikin wani irin yanayi na tashin hankali mai girman gaske sosai take jin zuciyarta da ruhinta suna faman kai kawo dauke da lamari mai matukar girma na tashin hankali. Hannayenta ta daura bisa goshinta tana dafewa gabadaya take jin duniyar na sauyawa a gareta gabadaya take jin komai na kara cakuɗe mata sosai take jin lamarin da Baseera ta sanar mata ya samu gurbi mai girma a sassa na zuciyarta wanda sam ba kwanciyar hankali a cikin sa. Numfashi take ja a hankali kafun ta ja jiki ta zauna bakin katifarta idanuwanta sun kaɗa sun yi jajir kamar wacce aka zubawa barkono. Bata san me zata yi ba, bata san mai ya dace tayi ba, ta tabbata lamarin nan zai iya narkar mata da zuciya har ma da gangar jiki sosai ta kasa gasgata abin da take ji a zuciyarta sosai take karyata kanta wanda bata san mai yasa haka ba ta tabbata zuwa yanzu ya kamata ta yarda da komai ta anshi komai a yarda ya zo sai dai kuma hanzarin da tayi ba gudu bane domin kuwa tana kallo kwaɗo yana shirin yi mata kafa kafar da take zaton in har yayi mata ita to komai ma ya rigaya ya gama faruwa. Mikewa tayi cikin rashin kuzari tana faman sakin huci mai zafi da take jin sa tun daga kasar zuciyarta yake busowa bakin kofa ta tokare Umma da take kallo dake zaune tana gyarawa Mu'azzam riga gefe guda ta zauna tana mai duban su amma a badinance zuciyar ta can wani waje ta cilla ta mai nisan gaske tana gayyato abubuwa masu yawa tana ajje mata a filin zuciyar tata. Umma ta lura da ita amma bata nuna ta ganta ba sosai take jin tausayin 'yarta ta a zuciyarta sosai yanayin da take ciki yake taɓa mata zuciya amma ta rasa ya za tayi ta rasa wani irin hali Mariya ta daukarwa kanta wanda ba a iya gane me ke faruwa da ita ba nisawa tayi bayan ta saki Mu'azzam yayi hanyar waje domin yin wasa ta dubi dakin su Goggo Marka kafun ta juya da hankalinta sosai kan Mariya da tayi tagumi da hannu daya idanuwanta akan Umma wanda sam ba ita kuma hankalin ta yake kai ba. "Mariya". Umma ta fadi murya a kasa cike da natsuwa da nuna rashin wasa kafun ta nisa ba tare da Mariya ta ansata ba. "Ban san ya zan dubi lamarin ki ba, ban san a wani mizani zan ajje komai naki ba, amma sosai zuciyata ta cilla wani bigire mai girma akan yanayin ki. Kin boye abin da yake damunki kina kiɗin ki kina rawar ki ke da zuciyarki a tunanin ki hakan shine daidai ko?". Girgiza kai tayi kafin ta nuna da hannu a lokacin Mariya ta dago idanuwanta ta na sauke su akan Umma kafin daga bisa ta kau da su. "Ban san mai ya canza miki halin ki ba, ban san mai ya sauya miki rayuwa ba, nidai na san ba haka kike ba, ni dai na san ba wannan halin kika ta so dashi ba, amma lokaci guda kin sauya komai na ki ya canza kamar ba Mariya ba. Zuciyarki...ina Zargin Zuciyarki da kuma abin da ke cikinta don na tabbata akwai abin da ya shigar miki zuciya ya canza miki komai na ki na tabbatar da hakan a raina, amma ki kasa faɗi mani a matsayina na uwa gareki baki da wata shaƙiƙiya wacce ta dace ki kai wa kukan ki da neman mafita kamar ni baki da kowa ba ki da wanda zaki kai wa kukan ki kamar ni amma Mariya kin yi watsi da wannan damar wanda ita kadai ce hanya mafi dacewa dake a filin duniyarki". Nisawa tayi kafin ta dubi in da take jin motsi a bayan ta Hafsat ce tsaye ta tokare bakin kofa ta zuba masu idanu kafin ta kau da kai gefe guda ita Umma nuna wa tayi kamar bata ganta ba Mariya dake zaune itama sun ga juna a tsakaninsu su zubdawa junansu kallo raini kafin Mariya ta kau da kai tana mai kokarin mikewa kan kafafuwanta. Bata hanata b domin ta sani ganin Hafsat ne ya sakata mikewa ta shiga daki ita ma mikewa tayi ta bi bayanta. Zuciyarta taji tana sanar da ita da ta fadi abin da ke cinta a rai amma tsoro da yarda Umma zata dauki lamarin ya hanata motsawa sai gyaɗa kai take yi kamar wata kadangaruwa Umma na binta da kallo. "Ba zan takura miki ba domin bana son nima a takura min bana son takura ga kowa domin takurawa tana iya sawa kiyi mani karya ki fada min abin da bashi ne ba ni kuma ba zan so hakan ba na barki har zuwa lokacin da kikayi ra'ayi don kan ki". "Ehem...Umma...". Da sauri ta daga mata hannu ganin yarda ta fara kalato furucin da zatayi kamar wanda akayi wa dole ganin yanayin da Umma tayi ya sanya ta tsuke bakinta waje daya idanuwanta su tara kwalla kadan. ****** Kallonta yake yi da wani irin yanayi mai haifar masa da wani lamari mai girman gaske tun daga tushen zuciyarsa da ruhi yake jin yanayin gangar jikinsa da jijiyoyin jikinsa gami da ɓargo suna ansar wani sako mai girman gaske. A hankali idanuwansa suka shiga lumshewa kamar wanda barci yaci karfinsa kafin ya sake buɗe su sosai akanta kafin ya kau da kai yana jan numfashi yana haɗiyeshi da kyar. "Mariya...". Kau da kai tayi daga kallon da take masa tun dazu mai cike da tuhuma da zargi kafin lokaci guda ta galla masa harara wacce ta sanya shi shanye abin da yayi niyar fadi. Jikinta sosai ya ansa da yanayin muryar da yayi amfani da ita wajan ambaton ta amma bata bari hakan yayi tasiri a zahirin ta ba. Juya tayi da zubar kowa gida zuciyarta da bugawa da yanayi na fargabar abin da zai je ya dawo ta san bata yiwa kanta adalci ba ita akaran kanta ta san haka amma bata san mai yasa komai take kasa saita shi ba ita da zuciyarta. Zuciyarta sosai take kara buɗewa da lamarin amma ita taki ba da kai bori ya hau numfashi take ja tana jin yarda kamshin turaren jikinsa ke bula ko wani sashi da lungu na cikin hancin ta yana haurawa cikinta yana hautsina mata kwanya da guntun tunanin da take ta kokawa dashi tun dazu. Bata san shi ne ba da ba abin da zai sata fitowa har ta dubeshi har yayi kokarin kara rikita mata lissafi duk da tana kaunar sanyashi a idaniyarta amma kuma kuncin da take ji game dashi yafi garwashin wuta a gareta zafi. " A tunani na ban yin tsammani na kai har haka a wajan laifi ba a wajan ki ko da yake ban yi mamaki ba tun da duniyarki ta kubuce ta daina tunanin wani mai kama dani komai sunana". Numfashi taja gami da tsayawa daga takunta da take yi wanda take jin jikinta kamar yana narkewa yana watsewa a kasa juyawa tayi idanuwanta na sauka a nasa da wani irin yanayi wanda lokaci guda ya haifarwa da zuciyoyi biyu abu iri guda har ya kusan tona sirrin da yake a ko wani dayan su. "kana kokarin daura min laifin da ban san dashi ba kana kokarin hukuntani akan abin da ban sani ba...". "Ba magana bace wannan ya kamata ki daina yin ta kin ji ko!". Ya fadi muryarsa da sauti a ciki yana takowa gareta sosai numfashin su yake dukan juna kafin Mariya ta kau da kai cikin kasalallan yanayi. "Akan mi zaka ce ba magana bace kai ne dai kake raina ta amma ni abin da na fadi shine daidai!". Ita ma ta fadi da zafi a muryarta kamar zata shako wuyarsa wani irin zafi da raɗaɗi take jin zuciyarta na haifarwa mai girman gaske. da mamaki yake dubanta jin yarda take masa magana murmushi yayi mai ciwo kafun ya kara kusanto ta. "Mariya". Ya kirata bata ansa shi ba illa dubansa da ta sake yi tana jan numfashi. "Kace ban cancanta da na tsaya ina kula samari ba har su zama abokan rigima ta yanzu kai mai ya kawo ka nan har ka tsaya a nan kake magana dani har kake daga min murya kenan kai ma kana sahunsu?". Runtse idanu yayi kafun ya buɗe su lokaci guda sun kaɗa sun yayi jajir. Bai san ta wacce hanyar zai dubi Mariya ba bai san mai ya dace yayi mata ba da zata gane in da ya sanya gabansa take ganewa taki fahimtarshi shi kuma ya rasa gane ta ina zai bi domin fahimtar da ita komai bai koma ya sanar da ita bai san ta yaya zata fuskance shi ba yana tsoron abin da zai je ya dawo. Takun da suka ji na takalmi ne duk ya dawo dasu daga dogon nazarin da su ka fada su duka dubanta suke yi da mamaki Baseera ce tsaye hannayenta sarke a juna fuskarta sanye da bakin glass No respect wanda ya hana tonuwar asirin yanayin da kwayar idanuwanta suke ciki amma daka kalleta zaka hango wani kwantaccen murmushi mai girman gaske a fuskarta ta a hankali ta shiga takowa har ta iso in da suke tsaye sai da tayi musu kallon tsaf! kafin tayi kasa da glass din tana duban Mariya wacce ita ma ita take kallon da wani yanayi wanda ba yabo ba fallasa. Murmushi tayi mata kafun ta dubi Dr.Karami da yayi fakare yana kallonta kashe masa ido daya tayi wanda komai da tayi din akan idon Mariya ne hakan ya sanya ta juyar da idanunta jin yarda kirjinta ke ansa sautin bugu kamar zuciyarta zata faso kirji ta yo waje wani tukuki bakin ciki da takaici taji yana taso mata yana turkewa a makoshi numfashi ma daƙyar take jan sa idanuwanta lokaci guda sun kaɗa sun yayi jajir. Motsa baki ta shiga yi kamar zata yi magana amma ina! ta kasa zuciyarta da take jin tayi nauyi kamar zata tarwatse ta hanata aiwatar da komai takun da taga Baseera nayi zuwa ga Dr.Karami yakara hargitse mata tunani da sauri ta fara ja da baya tana kokarin kwasa da gudu kuka ne take jin yana zuwa mata mai karfin gaske wanda ta tabbata in har ta cigaba da tsayuwa a wajan ba kuka kadai ne zata samu zarafin yi ba har zubewa akasa sumamiya sai tayi. "Mariya". Baseera tayi saurin kiranta ganin tana kokarin barin wajan ta juya tana takowa inda ta tsaya cak! fuskarta da murmushi kafaɗarta ta dafa kafun ta kure da idanu sosai. "Uhmmm...". Hannu ta daga mata a zafafe tana turen hannunta da ta daura mata kan kafada. "Bana muraɗin jin komai daga gareki kin ji ko don Allah ki bar naji da abin dake damuna a zuciyata bana son karin wani Tension din a wannan lokaci...". "ki daina fadin haka domin duk maganar da kikeyi karya ce kawai zalla a cikinta kuma bata kai zuciyarki ba ni nasan haka idanuwanki gashi nan kuma suna karya taki da kan su don haka Tell me the trut I don like joking Mariya in kuma ba zaki iya fadi ba ni zan fadi a yanzu nan ba sai kin bata min lokaci kin bata naki ba". Gyaɗa kai Mariya ta shiga yi idanuwanta na kawo kwalla ji take yi kamar ta kurma ihu don takaici komai na Baseera haushi yake bata ta tsaneta tsana mai tsanani bata taba zaton zata tsani wani bawa a filin duniyar nan ba amma a yau ta tsani Baseera Babbar ƙawarta da take ji da ita a filin duniyar nan wanda bazata ce ga dalili ba. "Of Couse in ba zaki iya fadi ba ni ina damar da zan iya fadi". Juyawa tayi ta dubi Dr.Karami da ya gama shiga wani hali na ruɗani musamman yanayin da ya ga Baseera tayi masa ba karamin tayar masa da hankali yayi ba ya jefa zuciyarsa cikin tsanani ruɗani mai matukar firgita kwanya. "Ta kasa fada maka abin dake damun zuciyarta, ta kasa fuskarta ka ta sanar da kai komai ko da yake kai ma da naka kunshin na sirrin zuciya a tsakaninku ban san waye ya dace na dora a mizanin masu cutar kai ba". Baseera ta fadi fuskarta ba wasa tana kai komo a tsakaninsu sosai dukkannin su suka shiga ruɗani in maganarta wanda suka rasa in da ta dosa sosai zuciyoyinsu suka shiga harɓawa da lamari mai girma akan maganar sosai suka shilla duniyar nazari ko za su kwato kansu daga duhun da suka faɗa akan zancen nata amma sun kasa sai watsa mata idanu suke yi suna faman jan numfashi kwakwalansu na kara cakuɗewa da lamari mara sauki a zuciya da ruhi. Taku tayi a hankali ta isa wajan Dr.Karami da ya saki baki da idanu yana kallon ikon mai duka shi dai aka ran kansa bai san ina ta dosa da maganarsa ba amma zuciyarsa nayi masa zargi akwai wani sirri da ta sani a tsakaninsu. "Zuciyarka zata cuce ka in har baka yi wasa ba". Ta fadi tana dubansa tsakar idanu kafun ta murmusa da wani irin yanayi. "Kana sona Dr.Karami amma ka kasa sanar dani har ni akaran kaina na fahimta ya kamata ace baka yi wannan saken ba domin kuwa bana tsammanin zan soka domin ina da wanda nake so". Runtse idanu yayi lokaci guda yaji wasu kibiyoyin tashin hankali sun cakar masa zuciya kafun lokaci guda yaji duk wani sashi na jinin jikinsa yana tsayawa cak! da gudana komai na jikinsa yaji yana narkewa da tashin hankali buɗe idanuwansa yayi lokaci guda ya sauke su wajan da Baseera take tsaye wacce a wannan lokacin ta rigaya ta juya ta doshi inda Mariya take tsaye tana kokarin mutuwa zuciyarta na ta faman kai kawo wasu kaifaffun wuƙaƙe taji suna soke mata kirji da zuciya da ruhinta take ji su na babbakewa lokaci guda. Tsoro ne ya saukar masa lokaci guda ganin yarda Baseera ta doshi Mariya ya tabbatarwa kansa maganar da ta sanar dashi ita zata sanar mata tsoronsa daya taki fahimtarsa tsoronsa daya tayi masa fahimta ta baibai tare da yanke masa hukuncin akan wannan lamari ya tabbata komai kara kwaɓewa zai yi da hanzari ya fara kokarin takawa domin isa wajan domin sanin abin yi amma ina kafin yayi taku biyu ta isa wajanta har ta fara magana da ita mutuwar tsaye yayi lokaci guda zuciyarsa ta buga da wani tashin hankali gumi ya fara karyo masa mai dumin gaske komawa yayi da baya ya jingina da motarsa a daidai lokacin ya hango mota kirar Benz tayi Parking kuri yayi wa motar yana kallonta haka kawai yaji motar bata kwanta masa ba a zuciya har da mai ita karan kansa kafin ya gama guntun tunaninsa ya ga Dr.Aqeel ya bayyana ware idanu yayi sosai yana dubansa da mamaki wani kunci ne yaji ya zo masa wuya lokaci guda ya tsaya kafun zuciyarsa ta shiga bugawa da sauri-sauri kamar zata yo waje. "Kin ka sa fahimta,na fada ki kina cikin yanayi na so amma kin ki yarda sai faman wahalar da zuciyar ki kikeyi na tabbata ba zaki taba samun WALWALAR ZUCIYA ba har sai ranar da kika gasgata na sani Dr.Aqeel kike so amma kin kasa sanar dashi hakan". Wani irin duba Mariya tayi ma jikinta har rawa yake yi yana karkarwa bakinta ya shiga motsi ji take yi kamar ta shako wuyar Baseera ta turmushe ko ta samu sa'ida da wadannan banzayen lafuza da take fada mata bata san ya kayi ta san Dr.Aqeel take so ba bata san wa ya fada mata shi take so ba bata ya akayi har bakin Baseera ya iya tafka wannan saɓon mai girman gaske ba. Numfashi ta ja mai tauri kafun ta dube ta sosai da idanuwanta rinannu. "ya kamata kiyi saurin tuba ga Ubangiji tun kafin ya hukuntaki akan wannan saɓon da kikayi". Ta fadi tana faman nishi numfashinta take ji yana fizga kamar zai rabu da gangar jikinta gabadaya duban Dr.Karami tayi lokaci guda taji zuciyarta ta sake bugawa kafun ta dubi Baseera da take faman kallonta fuskarta da murmushi. "Karki sake zuciyata tayi gangancin fara ci miki mutunci karki ga laifina tun wuri ya kamata ki sauya maganar domin ba haka take ba". Dafa kafaɗarta tayi tana faman sauke numfashi ita jarumtar ta fara rauni bata san ya zata sauke lamarin nan da ta dauko ba mai girman gaske kwakwalwarta ta fara kamawa da wuta batayi zaton abin ba zai zo mata da sauki har haka ba ta dauka lokaci guda komai zai sauya za su karbi muradan zuciyoyinsu ashe fatanta ba zai tabbata ba burinta zai nakasa a wannan matakin tun kafin aje ko ina kau da kai tayi wasu kwalla suka taru mata kafin ta mai da su daƙyar tana faman jan numfashi duban Mariya tayi sosai har yanzu tana kan bakarta taki yarda da burin zuciyarta. Da dan hanzari Baseera ta juya ta koma inda Dr.Karami yake tsaye gabadaya abin duniya ya ishe shi tsoro yake yi yaji inda zance zai kwana shi da Mariya. "BAR RAINA ALLURA...". "...Domin kuwa karfe ce". Kamar daga sama Baseera taji muryar ta sauke zancen da ta dauko da sauri ta juya Dr.Aqeel ne yake takowa a hankali fuskarsa da yanayi na ba yabo ba fallasa hannunsa da Key din motarsa ya faman kaɗawa sosai ya tunkaro su kallan kallo suka shiga yi shi da Dr.Karami kallo ne na wani irin hali mai kama da 'a cike nake da kai, kana son kawo mani tsaiko a lamari na.' Harɗe hannayensa yayi a ƙirji lokacin da ya iso yana mai dubansu daya bayan daya kafin ya dire akan Mariya da tayi wujiga-wujiga da ita kamar wacce ta kwato kanta daƙyar daga bakin kura. "Bana tunanin wannan tsayuwar da kukayi akwai mafita a cikin ta maganar gaskiya ya kamata ku sani ni Mariya take so domin duk abin da kuke zantawa da yarda ke Baseera kike yi na san so kike yi ki hada tsakaninsu amma kin kasa to ki sani Mariya bata da wani wanda yake son ta take sansa tamkar yani...". "You don get Sense At All Dr.Aqeel ya kamata ka iya bakin ka tun kafin ya kai ka ga dana sani". Cewar Dr.Karami yana faman hirji jin abin da Dr.Aqeel yake fadi gaba gaɗi cikin gadara da isa. Murmushi ya saki yana mai watsa hannu sama kafun ya dubi Baseera. "Bana zaton Mariya zata so Dr.Karami domin kuwa bai nuna son ba ni na fara nuna mata so don haka ni zata ansar wa so". "Ba dole bane ka fara furta kalmar so ka yi tunanin kuma za a anshi naka son akan wanda ya so daga baya so ba ruwansa sai wanda ya burge zuciya ta aminta dashi zata so dadewa a so ba shi yake sanya a so mutun ba so a RANA DAYA yana iya samun gurbi sannan so yana iya wanzuwa zaman shekaru amma bai samun gurbi don haka ka sani GURBIN SO ba a ko wani waje ake samun sa ba sai inda ya dace". Gabadayan su suka juya in da suke sauraron zantukan na fitowa Huzaif ne tsaye harɗe da hannu yana faman dariya mara sauti har da 'yar kwallarsa a idanu a hankali ya shiga takowa yana mai cigaba da cewa. "Bana tunani don ka zo ka furta so kayi tunanin zaka samun GURBIN SO a zuciyar da ka furtawa so lokaci guda so daban yake sannan so sai inda ya ga ya dace zai shiga duk da dai shi kan shi so din ba ya lura da dacewa ko matsayi ko wata daukaka kafin ya farwa zuciya kana ganganci da kace so sai ya tsufa a in da ake furta shi yake samun gurbin zama ya kamata ka sauya tunaninka". Ya fadi ya mai duban su kafun ya dubi Mariya da tayi firgai-firgai da ita kamar wacce take jira ace kes ta kurma da gudu bata san lokacin da hawaye suka fara zuba a idanuwanta ba dumin su kawai taji tunda Huzaif ya tunkaro ta take jin gabanta na tsananta faduwa da tashin hankali mai girma so take yi ta saki ihu ko zuciyarta ta daina tsalle tsalle da babbakewa da take yi zuciyarta ta take ji tana kumbura cikin kirjinta komai na jikin ta take jin yana daukar zafi kamar roba cikin wuta ji take yi tana narkewa da tashin hankali mai girma gaske bata san wani bala'i bane kuma yake kokarin samun gurbi a yanzu bata san wani irin tashin hankali bane zai sanyota gaba a wannan bigire ta shiga uku ita a duniyarta. Saukar hannu taji a fuskarta ana dauke mata hawaye wani numfashi taja mai karfi kafin ta runtse idanuwanta ta buɗe su Huzaif ne yake dauke su da hankicif dake hannunsa dubansa take yi da idanuwanta masu kokarin rufewa da kwalla dubansa take yi gabanta na kara tsananta buguwa komai take ji ya kwance mata bata san ya za tayi ba zuciyarta take so ta buga ko zata mutu ta huta da wannan bala'in da take ciki kau da kai tayi lokaci guda ganin irin kallon da Huzaif yake jifanta dashi mai kokarin rikitata ta tsane shi tsana sosai amma bata san abin da yasa lokaci guda zuciyarta ta tuna mata da babinsa ba ta tuna mata da GURBIN da ta bashi a zuciyarta har yake kokarin buɗewa. "Yaa Rabbi". Ta furta can kasan makoshinta kafin ta dago kanta ta sake dubansa Dr.Aqeel ta hango ya tunkaro wajan kamar wani mayunwacin zaki sai faman hirji yake yi yana kara hura iska a hancinsa idanuwansa sun kaɗa sunyi yayi kamar anyi masa surace da Barkono hankali ta fara kokarin ja da baya amma ina kafafuwanta take ji kamar an turkesu a waje guda ko motsi basa yi. "Wai kai ba wani iri mutum ne? shin baka san in da so ya dace bane da yarda bai dace ba na lura kai ma dan takife ne a harkar so ka daina tunanin za kayi wani tsawon rai a harkar so tun wuri ka tattare tashin balagar kyankyasan ka da kake ji dashi sannan kake ganin karan ka ya kai tsaiko har kake tunanin TASIRIN SO zai zauna akan ka ni ne nan wanda so zai yi wa rana ba kai ba". "Me yasa kafi ye kaunar kan ka ne mai yasa kake son cutar da zuciyarka ne mai yasa kake son ajje GURBIN SO a zuciyarka bayan ka san wauta kake yi wa kan ka bana tunanin ka san meye so kafun ka shige shi a filin duniyarka...". Duban junan su suke yi kamar wasu mayunwatan zakuna sai faman kallon kallo sukeyi wa juna mai cike da tsananin rigima da tsanar juna. Bige hannun da Dr.Aqeel yayiwa Huzaif ne ya sanya shi tsagaitawa da maganar da yake yi yana mai murmushi a hankali kuma ya shiga duban Mariya kamar zai shige jikinta idanuwansa sarke da nata. "Kice baki Kaunata ki fadi su ji ba kya sona". Runtse idanu tayi tana jin zuciyarta na kara buɗe wasu kofofi har kashi uku wanda ta jima da kullesu gabadaya take jin su suna buɗe kan su da kan su dubansa tayi kafun ta daura hannu aka tana kokarin kurma ihu amma ina ihun ma yaki zuwa hawaye kawai suke mata ambaliya a daidai lokacin Baseera ta iso tana faman duban Mariya fuska a raunane. "Da matsala Mariya ban san ya zan sanar dake ba amma maganar gaskiya Dr.Karami ba so na yake yi ba ke yake so nayi wannan shirin ne akan cewa ko za ki nuna kishi ki fito ki sanar masa shi kike so kika kasa fadi masa...". Ji kake kau! hannun Mariya akan kuncinta ta shiga nuna ta da hannu tana faman tangaɗi kamar wanda ta sha barasa tayi makas gabadaya ta fice daga cikin hayyacinta. "Kina tunanin zan so shi ne bayan kin ce mani kuna soyayya kina tunannin maganar da kika fadi mani zatayi tasiri akai na ne ki bar ni kawai naji da bala'in da kuka jefa ni a ciki na san dama duk ba kwa kaunata dama na sani rakiya nayi duniyar nan na zo ne don kawai a tarwatsa min zuciya na mutu kowa ya huta burin ku ya cika Shikenan..Shikenan zan mutu yanzu zan mutu yanzun nan...". Kawai fadin maganganun take yi tana dariya idanuwanta na zubda hawaye da sauri Baseera ta isa gareta ta riketa sosai tana faman hade jikinta da nata wani kuka mai zafin gaske ta saki zuciyarta na faman a zalzala da zafin mai girman gaske. "karki yi saurin yanke tsammani Mariya so ya gaji haka...". Da sauri ta kwace kanta tana faman ja da baya tana sakin huci. "So ya gaji haka fa kika ce? dama haka so yake da bala'i a cikin sa, dama haka so yake da kayan guba a cikin sa, dama haka so yake da masifa a cikin sa?. tabbas na yarda SO DA RAININ HANKALI yake, na tabbata so akai na ya fara haifar da masifa, na tabbata akaina so ya fara haifar da bala'i, na tabbata akai na so ya fara haifar da cuta mara magani, tun kafin aje ko ina so ya fara min haka to ina kuwa in na fara zama ina yiwa so biyayya...". Goge fuskarta tayi kafun ta dubi Dr.Aqeel da Huzaif da suka zuba mata idanu cikin halin ta shin hankali. "Kace kana so, kai ma kace kana so sannan kuma shima...". Sai kuma tayi shiru tana duban Dr.Karami da ya zama wani butum butumi gaɓadaya ya kasa motsi a yarda yake tsaye kawai numfashi ke fita a jikinsa amma ya tabbata ba abin da yayi saura mai motsi a ko ina a jikinsa bai taba tsammani zai shiga tashin hankali irin na yau ba bai taba zaton zai ga bala'in rayuwa ba irin na yau sai yau ya kara ganin wautarsa da gangancinsa ya kara tabbatar da maganar hausawa nacewa 'BAR RAINA ALLURA KARFE CE' in ya cire rashin dacewa ya cire ganin kankata ya dauko ma'aunin so a yarda yake ya ajje a zuciyarsa da duk haka bata faruwa ba ga shi yanzu abin da ya raina yana kokarin haifar masa da CIWON RAI mara magani. "Baseera ban san wata ƙaddara bace ta jingino mani wadannan mutanan ba, ban san mai yasa ALKALAMIN ƘADDARA da ya tashi rubuto min tashin hankalin rayuwa ba, ya jehomin ta hanyar so...". Da sauri ta iso gareta tana mai rufe mata baki. "Karki ce haka ki dauki komai a matsayin jarabawa sannan kuma ƙaddararki ta rayuwa...". "zan dauki komai a matsayin ƙaddara amma ban da lamarin na domin na tabbata bala'i ne bala'i mai ansa suna bala'i domin na tabbata duk ikirarin da suke yi suka ce suna sona ba wanda yake tausayi na a cikin sun in da suna sona ba za su so su gannin cikin bala'i ba amma da yake su masu son kai ne ko wanne ya dauko tawagar rigunan bala'in sa ya jinginawa rayuwata". A hankali ta fara taku tana kokarin barin wajan kafin ta tsaya ta juya tana duban su. "UKU BALA'I kuka dasa min a rayuwa domin ba zan kira shi UKU ALHERI ba kuma ina so ku sani dukkan ku ina son ku ko wannan ku na saka shi a zuciyata yanzu abin da ya rage a tsakanin ku sai ku zo ku dandatsani kowa ya dauki kason sa". Ta na gama fadin haka ta juya cikin sassarfa kuka na kara tunkodo mata zuciya hannayenta ta saka ta toshe bakin ta har ta fada cikin gida a zaure ta durkushe tana faman jan numfashi hawayen da take so su zubo mata sun ki zuwa kukan ma lokaci guda ya tsaya cak! kanta ta daga sama ta runtse hannayenta duk biyu ta dora a saman kirjinta tana faman haki kafun lokaci guda numfashinta ya dauke idanuwanta suka ƙaƙƙafe. Ihu Baseera tayi lokacin da ta biyo bayanta taga halin da take ciki da sauri ta isa gareta ta kai hannu tana kokarin jinjingata amma ina lokaci guda ta bingire kasa ba alamun numfashi hakan ya kara sanyata sake kurma wani uban ihu tayi waje da gudu a daidai lokacin su su duka ukun sukayo cikin soro Dr.Karami har yana cin karo da Baseera da sauri ya rikota tana kokari faduwa ya fada cikin soron a daidai lokacin kuma Umma da Goggo Marka gami da Hafsat suka duro cikin soron ganin Mariya asheme ba alamun rai ya sanya kowa sakin salatin Dr.Karami yayi kanta yana kokarin daukarta Dr.Aqeel yayi saurin riko shi fizge kansa yayi yana yin kurin sake kaimata sura Umma dake tsaye ta shiga duban su su duka ba wanda bata sani ba da sauri ta isa wajan da Mariya take yashe ta durkushe tana mai dundubata kafin da dago ta dube su da hawaye a fuskarta. "Yaa Allah". Ta fadi tana mikewa kafun ta dubesu ba tare da wani firgici ba. "Sai ayi kokarin yi mata suttura a kai ta gidanta ko saboda Allah yayi mata cikawa". Ba wai Dr.Ƙarami da su Dr.Aqeel ba kadai ba hatta Baseera sai da numfashinta ya dauke. Saukar ruwan da suka ji ne ya dawo da su hayyacin su Hafsat ce dauke da rusheshen baho tsaye tana faman yatsine fuska sai faman kallon uku ahu take jifan su dashi take yi gabadayan su a firgice suka dawo hayyacinsu sai faman kara kaina sukeyi a tsakanin su sun rasa abin yi ma Dr.Karami ya ja tunga ya tsaya yana mai da numfashi kafun ya dubi in da Mariya take yashe har zuwa lokacin dai jiya-i-yau ƙura mata idanu yayi sosai yana kallonta tun daga babban dan yatsanta har zuwa kanta gata nan sambal! Kansa ne ya shiga juyawa yana dawo masa da maganganun da Umma tayi da karfin gaske ya toshe kunnuwansa yana furta. "Nooooo!". Kafin lokaci guda ya sureta kamar wanda ya dauki 'yar tsana ya fice da ita daga cikin soron gidan dukkan su suka goya masa baya illa Goggo Marka da Hafsat dake tsaye suna duban su da wani irin yanayi da nuna halin-ko-in-kula ga lamarin Umma kuwa cikin gida ta koma ta dauko mayafinta ta yo waje ko kafin ta iso ba wanda ta tadda nan ta jin gina da bango tana faman ajiyar numfashi mai zafi kafin ta rintse idanuwanta ta buɗe su. "Allah ga bayinka kai ka san abin da yake damun su a filin duniyar nan kayi musu maganinsa". Tana gama fadin haka ta juya cikin gida cikin yanayi na rashin tabbas din 'yar ta ta domin kuwa ta san ko sun kaita asibiti sai dai su dawo da ita domin tuni ta tabbbatar Mariya ta shuri burji rai yayi halinsa. *_Ina bukatar ra'ayoyinku Makaranta da duk wani masoyina na labarin nan kafin muje ga cigaba ina so duk ku antayo min wani tsokaci game da labarin da ya danganci sharawa ko gyara_* *_KAMALA MINNA_*😍😍😍 [9/6, 1:59 PM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA ARBA'IN DA DAYA. Saura kadan Hafsat ta bangaje Umma lokacin da ta karasa cikin gidan. domin a soro ta tadda ita, tana faman leken duk abin da ke faruwa. Dubanta tayi kafin ta girgiza kai, ta wuce ta cikin yanayi na kunci da bakin cikin halin-ko-in-kula da halin ƙi da suke nunawa ga 'yarta musamman Hafsat da ƙiri-ƙiri ba kunya ba tsoron Allah take fitowa fili ta fadi mugun nufi akan Mariya da wannan tunanin ta isa ciki gidan. zaune ta hango Goggo Marka kofar dakinta tana faman ɓarar gyaɗa tana tauna tana wakar barmana coge ganin Umma ta shigo ya sanyata yin shuri tana dubanta. "Ai kawai aje a sanar da jama'a da Malam Nata'ala, domin yin jana'izarta tunda an shuri burji". Wani tuƙoƙine da bakin ciki ya tokarewa Umma wuya lokaci guda a rana daya yau taji bazata iya shanye wannan cin zarafin da cin fuska da ake yi mata ita da 'yarta ba dubanta tayi ƙwalla cike da idanu. "ai ƙaddarar mutuwa tana kan kowa kuma wanda ya mutu da da yanzu duk ba hanzari sukayi ba wajan barin duniya". Wani uban ashar Goggo Marka ta danno kafin ta miƙe jikinta har ɓari yake yi saboda tsabar masifa kamar jira take yi tayi mici-mici da idanu zanin jikinta har yana kokarin kwancewa ta watsar da gyaɗar dake hannunta. "Ni kike fadiwa haka Habeeba eh lallai duk mai sauran rai a duniyar nan yana DA SAURAN KALLO ke har kin yi bakin da zaki yaɓa mani magana ke har kin isa". Ta shiga sababi har ta isa gare ta tana dungure mata goshi a daidai lokacin Hafsat ta iso cikin gidan jin hayaniyar Goggo Marka ganin abin da ke faruwa ya sanyata hanzarin karasowa tana duban Umma uku ahu tana faman yatsine fuska kafin ta ja dogon tsaki kamar harshenta zai tsinke ta ja hannun Goggo Marka suka bar wajan tana mai fadin. "yo ana tara kartan mazaje ba dole mutuwa tayi hanzarin zuwa ba tunda jaraba da masifa ta cika zuciya ko wani kare da doki nata ne mu dai Allah ya tsare mu da kamayamaya kar ajona mana mu tafi wajan likita yayi ta aunamu kamar yadi". Mamaki ne ya cika Umma jin furucin da 'yar cikinta kamar Hafsat take fadi mata duk da dai bashi ne karon farko ba da ta fara dubanta tana mata izgilanci da kalamanta amma taji maganar yau sosai har kokwan ranta girgiza kai kawai tayi ta ja kafafuwanta da taji suna kokarin gagarar daukarta ta shiga cikin daki cike da tashin hankali mara yankewa abun ya zame mata GOMA DA ASHIRIN a filin duniyarta. ******* Kai kawo kawai suke yi a Reception ɗin asibitin gabadaya hankalin su a tashe yake in ka zare Dr.Karami da yafi kowa fidda tsammani dafatan samun Mariya a yarda ya dauko ya saka a mota ya tukota zuwa asibiti ba tare da ta yi ko da motsin ba hakan ya kara hautsina masa tunanin kwanya ya firgita masa duk wani fata da burin da yake dashi akanta yayi dana sani da takaici kuma akan abin da yayi na rashin bayyanar da abin dake zuciyarsa tun kafin lokaci ya kure masa sannan ya ga bakin kansa akan yarda komai ya hautsine komai ya dakule duk a gabansa ba tare da yayi wani fata ko yinkurin yin wani abu ba ya sani Mariya zata tsane shi tsana mai tsanani a filin duniyar nan dalilin kin bata dama da yayi abin ya zame masa goma da ashirin ya tabbata har da zancen Baseera ya so kashe ta yasani zata dauke shi a wani dan ta'adda makashin rai cikin wahala ba tare da cuta ko samun matsala ba. Bai san ya lamarin zai zo masa ba amma ya tabbata sai yafi kowa shan kashi a cikin su dole ya fuskanci kalubale mai tsaurin gaske dole ya fara tanadar makaman yaki domin guntule duk wani abu da zai kawo masa hari na kalubalen da zai fuskanta. Numfashi yake ajjewa a hankali kamar wanda ranshi yaso barin jikinsa daga baya ya tsaya kuma yake mai da numfashi duban su yake yi daya bayan daya yana ajjewa kowannen su kallo na irin yarda yake jin kowannan su a zuciyarsa da Dr.Aqeel suka hada ido ya jefa masa kallon takaici kafin ya kau da kai lokaci guda cike da bugawar zuciya. Motsin buɗe kofar da akayi ne ta dakin da aka kargame Mariya a ciki ya sanya dukkaninsu mikewa kan kafafuwansu cikin hanzari da firgici na rashin abinda za a zo dashi a matsayin sakamako a junansu. Dr.Karami ya fara tarar likitan da ya fito yana faman sharce gumi kafin ya dubesu su duka da yanayi na rauni na sosai. "Kai ne Dan'uwanta?". Likita ya fadi yana mai duban Dr.Karami da ya iso gareshi a hargitse kamar mahaukacin da ya balle daga gidan mahaukata. Gyaɗa kai ya shiga yi yana faman nishi kamar wanda akayi wa dole. Sosai likitan ke dubansa yana son gane tashin hankalin da yake ciki bai gama yanke hukunci ba yaji an kwala masa kira kamar daga sama da sauri ya juya Nurse din da suka shiga tare ne ta yafito shi da dan razana a fuskarta da sauri ya juya cikin sassarfa yana kokarin tura kofar Dr.Karami ya sanyo kai shima zai shigo amma sai likitan ya dakatar dashi ta hanyar yi masa kallo gami da girgiza kai sa'annan ya mai da kofar ya rufe. Dr.Karami ji yayi kamar ya kurma ihu inda yana da raunin zuciya ba abin da zai hanani shi rushewa da kuka domin yanayin da yake jin zuciyarsa ahalin yanzu yafi komai ciwo ji yake yi zuciyar kamar ba tashi ba ba abin da yake yawo a ciki illa wani irin tausayi da mahaukacin son Mariya ji yake yi kamar ya kwato duk wata cuta da take kokarin kashe masa ita ya dawo da ita jikinsa ko zai samu burinsa da fatansa ya tabbata a filin duniyar nan haɗe kai sa yayi da bango yana faman numfashi kamar wanda yayi gudun ceton rai ko da yake za a iya kiran hakan da gudun ceton rai don yarda yake wassafa abin kamar tashin alkiyama yake kallo duk wani tashin hankali da yanke tsammanin farin ciki ya tabbata akansa a daidai wannan lokacin. Ji kawai yayi kafafuwansa na kokarin kasa daukarsa bai san lokacin da ya sulale zuwa kasa ba ya zauna kamar wani kayan wanki idanuwansa yaji suna wani yaji-yaji zuciyarsa na zafi da raɗaɗi a hankali ya fara ambaton sunan Allah a bakinsa yana faman sakin huci mai zafi. Shigar likita cikin dakin ya tadda Nurse gaban na'urar da take tafiyar da yanayin wanzuwan numfashin mara lafiya da sauri ya isa wajan ganin numfashin da ya samu ya kwato da kai da taimakon Allah yana kokarin kufcewa aka karo na ba adadi da sauri ya isa wajan yana duban na'urar kafin ya sauke dubansa kan Mariya dake kwance sambal wacce bata da mara da gawa ga Oxgyen da yake kargame a hancinta a hankali ya kai hannunsa saitin makoshinta da kirjinta yana tabawa komai yaji ya sauya ba a yarda ya barshi ba idanu ya zaro kafin ya sake duban na'urar wacce take nuni da numfashin yana kara samun ragwanta da sauri ya zaro abin auna mara lafiya ya jona mata a kirji kafin ya soka abin a kunnuwansa lokaci guda ya zare ya isa ga na'urar yana tabe tabensa tun yana yanke tsammanin samuwar komai har ya fara firgita da yanayin numfashin da sauri ya isa ga Mariya yana dubanta ita kanta Nurse din abin ya fara fidda mata da tunani daga kai da sauri ta iso wajan tana duban likitan kafin tayi wani yinkuri wanda take fatan samun daidaituwar komai likitan ta kalla wanda ya gama firgita sosai a hankali takai hannayenta saman kirjin Mariya ta shiga dannawa da sauri-sauri a daidai lokacin Na'urar tayi dan kara tafiyar numfashin ya fara canzawa cikin yanayi na farfadowa daga suman da yayi hakan da Nurse din ta ga ya bata daman saurin cigaba da danna kirjin Mariya kamar zata burmasshi ita da gadon shi kuwa likitan gaban Na'urar ya isa ya shiga dube-dube yana kokarin saita komai. Lokaci mai tsayi suka dauka suna abu daya gabadaya sun gama hada gumi da fidda tsammani da fata akan Maryia domin tafiyar numfashin ma yaki gaba yaki baya iya kokarin su sun yi amma abun ya ci tura lokaci guda fuskar Nurse din tayi rauni kamar wanda zata fashe da kuka danna kirjin Mariya take yi zuciyarta na kara karyewa da rauni mai girman gaske hawaye lokaci guda suka shiga zubo mata ba ta bi takan su ba illa kokarin na ganin ta ceto numfashin wannan baiwar Allah a hankali ita kanta numfashin nata da kirjinta su fara sauyawa da bugu ganin numfashin ya fara yin kasa ta tabbata yayi kadan gabadaya sai dai wata amma ba Mariya ba kokari ta kara kalatowa da jarumta ta shiga dannan kirjin Mariya tana duban Likita da komai yake shirin wargaje masa kamar ƙyafta idanu Na'urar ta saki wani sauti lokaci guda numfashin ya shiga tafiya da sauri-sauri yana cike gurbin da bai kai ba lokaci guda ya dawo yarda ake so Mariya dake yashe Nurse na danna mata kirji wani yin kuri tayi kamar wacce aka bugo kasan gadon tayo sama sannan ta koma ta sake yin wani yinkurin kafin nan ta koma da sauri Nurse ta shiga rirrike ta. Gwauron ajiyar numfashi likita yayi yana dauke gumin da ya tsatsafo masa a fuska kafun ya iso ga Mariya da take ta faman jan numfashi ta hanyar Oxgyen dubanta ya shiga yi kafun wani lokaci yayi kokarin ganin komai ya daidaita duban Nurse yayi tare da yi mata jinjina ganin yarda tayi firgai-firgai da ita kamar wacce ta kwato kanta daga bakin kura. Ya jima yana bakin kokarinsa kafun ya saita komai sannan ya fice daga cikin dakin. Da hanzari Dr.Karami ya mike daga yashen da yake gefen guda yana faman cizon laɓɓa kamar mace mai nakuɗa sosai yake duban likitan cikin yanayi na tabbacin abin da zai fada masa mai dadin ji ne ko sauraro sosai tsoro da firgici su ka bayyana a idanuwansa kirjinsa da zuciyarsa sautin bugunsu yana ansa wa cikin gangar jikinsa ruhinsa kuwa ji yake yi kamar ya shuri burji ya bar jikinsa ya zama matacce. Sai da ya gama firgicinsa yana ta faman jan numfashi magana yake so yayi amma ya kasa sai haɗe hannayensa yake yi waje guda yana matsewa yana faman mazari kamar wanda ake kaɗawa gangi shi kansa likitan tsayawa kallonsa yayi sosai ya fuskanci akwai wata alaƙa mai karfi tsakaninsa da Maras lafiyar wanda hakan ya kasa boyuwa a gareshi. "Doctor don Allah...". Furucin da Baseera take kokarin yi kenan lokacin da ta hango fitowar likita gabadaya ta gama firgicewa sai faman jan numafshi take yi bakinta na ɓari ta hadiyi yawu mai tauri kafin taja fasali ta sake dubansa tana goge hawayen da suke ta faman ambaliya a fuskarta. "Karka ce mani ta mutu domin kuwa ba wai ita kadai ta mutu a filin duniyar nan ba akwai rayuka masu muhimmanci a duniyarta da za su salwanta wanda kuma har dani bana tunanin zan iya juri da yin TAWAKKALI in Mariya ta zarce in da ba a dawowa domin na tabbata ba zata yafe mani ba na tabbata ina da laifi mai girma wanda na san zuciyarta ta kunsa kuma ba zaya yafen ba...". Nishi tayi tana faman hade hannayenta waje daya alamun roko kafun ta dubi Dr.karami da ya runtse idanu kana hango yarda kirjinsa ke dokawa kau da kai tayi tana kara jin zuciyarta na karye da tsananin tashin hankali mai girman gaske. "Karka ce mani ba zan sake jin sautin Muryarta ba karka ce mani ba zan sake cigaba da rayuwa da ita a filin duniyar nan ba don Allah Doctor kace wani abu". Dubansu yake yi daya bayan daya har da su Dr.Aqeel da Huzaif da suke ta faman kokawa da numfarfashinsu tashin hankalin su na daduwa gabadaya sun gama firgicewa sun gama yanke tsammani da numfashin Mariya a doron duniyar nan. Nisawa yayi kafun ya dubi Baseera dake ta faman rusar kuka. "Ki tsaurara kalaman ki kamar ba 'yar musulma ba ko Mariya mutuwa tayi bai kamata ace kina irin wannan maganganun ba dole ki saka tawakkali a zuciyarki dole ki anshi ko wacce irin ƙaddara ce ta faɗo duniyarki...". "Ya isa haka Doctor". Dr.Karami ya tare shi yana faman jan numfashi ya buɗe idanuwansa akan sa sosai sun kaɗa sunyi jajir jijiyon kansa duk sun fito sunyi ruɗu ruɗu. "Ya kamata kayi abin da zai kawo kwanciyar hankali da natsuwa a garemu duk wani dogon turanci ba zai tsayar da kalamin da kake cewa bai dace ba abu daya zaka fadi wanda duk zai kau da rashin hayyacin da muke ciki". Magana yake amma da ka kalle shi zaka gane akwai dauriya da juriya a zuciyarsa amma in ba don haka ba da tuni ya zube akasa a hankali ya shiga lumshe idanuwansa ya na matsawa jikin bango ji yayi kafafuwansa na kokarin zubda shi kasa jingina yayi da bangon zuciyarsa na harbawa da sauri-sauri. "Ban san wa zan fuskanta ba". Likitan ya fadi yana dubansu domin gabadaya sun gama rikita shi da rashin hayyacinsu. Dr.Aqeel ya tako gareshi da hanzari ya roko hannunsa sosai. "Fada min ni ne makusancinta me ke damun ta...". Wani haushi ne da zafin zuciyata ya turnuke Baseera jin abin da Dr.Aqeel yake fadi dubansa take yi da idanuwanta duba na raina hankalinka cizon laɓɓanta tayi kafin ta kara dubansa sosai. "Mukusanci fa kace?...". Ta fadi tana dariyar da ta fi kuka ciwo kafin ta sake cewa. "kawai cewa zakayi kana cikin yan ta'addan da ke kokarin salwantar mata da rayuwa". Da sauri ta dubi likita. "Don Allah na rokeka karka saurare shi kar kace dashi komai game da Mariya domin ba amfanin da zai iyayi akanta illa ya kara turbudata cikin tashin hankali duk da sun yi ajalinta". "Doctor Please Rabu da su don Allah ni ne mai kaunar ta nine masoyinta na asali...". "Karya kake yi..wai don Allah me kuke son mai da ita ne ta shuri burjin ma ba za ku daina hauka kuna saka mata bala'i ba". Baseera ta sake katse Huzaif da ya iso shima yana cewa wani abu. "Yaa Allah wai anya kuwa kalau kuke anya kuwa ba kune kuka saka zuciyar baiwar Allah nan take kokarin bugawa ba haba mana menene haka kuke yi gabadaya kun rikita ni na rasa wajan da zan duba na fuskance shi". "Doctor ni zaka fuskanta". Kamar daga sama suka tsinkayo muryar Dr.Karami cin sauti mai ansa amo sosai da sosai a hankali ya fara takowa da wani irin yanayi tattare dashi karkasahinsa da mazantakar da yake tattare da ita jarumta da zuciyarsa ta gayyato masa duk ya ajje su saman fusakarsa lokaci guda duk wata kwalla da take kokarin samun gurbi a idanuwansa ya haɗiye su yanayin takunsa da sautin da takalmarsa ke bayarwa ya sanya likitan dubansa duba na sosai da sosai zuciyarsa ta yarje masa da cewa wannan shine makusancinta na kut da kut. Gaban likitan ya zo ya tsaya sosai kan kafafuwansa duk da raunin da suke kawo masa hakan ya jajir ce yana jin yarda yake tsoro da kuma fargabar ansar abin da likitan zai sanar dashi zuciyarsa narkewa take yi da tashin hankali wani fili mai girma da ya jima da gina shi ya ajje Mariya a ciki ji yake yi yana kara buɗewa da wani yanayi na so mai girma sai yau sai yanzu a daidai wannan lokaci ya ya gama AMANNA akan son da yake yi wa Mariya sai yau ya gasgata da gaske yana sonta so mai ansa suna so sosai yake jin zuciyarta ta gama ajje GURBIN SO ako wani sashi da fanni na cikin ta ya yarda ya kuma amince son Mariya A JININSA YAKE a jikinsa yake son Mariya shine farincikin rayuwarsa son Mariya ya gama tafiya da duk wani imaninsa na filin duniyarsa. Likitan da yake can kasa da Dr.Karami ya dago kai ya ajje idanuwansa akan nasa sosai yake hango wani lamari mai girman gaske lamarin da a lokaci guda ya ba shi suna da SO sone aciki son wanda son yake tsammani ita ce akwance ita ce wacce aka kawo bata da lafiya... "Ni ne makusancinta ni ne dan'uwanta ne ni komai nata a filin duniyarta ni ne farincikin rayuwarta ni ne...". Kau da kai yayi da sauri jin zuciyarsa na kokarin harbawa da wani irin so mai girma ba ya tunanin zai iya daukar abin da likitan zai fadi a wannan lokaci yana tsoron yace masa da gaske ta mutu yana tsoron yace masa AN KASHE SO don ya tabbata son sa za aka kashe farin cikinsa zai kare a filin duniyarsa Mariyaaa ce. "Akan wani dalilin zaka dauki wannan lamarin ka jingina wa kanka a matsayinka na wanda bai san WACECE ITA ba akan mi zaka ce kai ne makusancinta akan me zaka ce kai ne kafi kowa kusanci da ita". Dr.Aqeel yake fadin haka a zafafe yanayin sa kawai zaka kalla ka gane danyen so da yake ji na Mariya sosai zaka fuskanci zallar so mai ansa suna so a filin fuskarsa har da gurbin zuciyarsa. Nishi yake ajjewa yana kallon Dr.Karami da wani irin yanayi kafin yayi taku daya zuwa uku ya daga dan yatsarsa daya ya nuna Dr.Karami dashi. "Ka sani in akwai wanda yafi cancanta ya zama makusancinta da komai nata ni ne nan!". Ya fadi yana nuna kansa yana dukan kirjinsa da karfi cikin sauti mai ansa amo sosai har jijiyoyin kansa na fitowa duk da duhun fatar da yake da ita. "Bana tunanin a filin duniyar nan akwai wanda ya dace da ita kamar ya ni ka sani Dr.Karami ta dalilina kasanta ta dalilina kansan wacece ita kafin kasanta ni ne nan na fara saninta kuma tare ka ganmu!". Ya sake fadi cikin hargagi kamar zai kaiwa Dr.Karami duka ya juya ya dubi likitan yana kokarin yin magana Baseera ta daga masa hannu cikin tsananin haushi da takaici. "duk wannan abin da kake yi IHU BAYAN HARI ne mutuniyar da kuka kashe har kake da karfin zuciyar da zaka zauna kana dambe akan ta mutuniyar da kuka zama ajalinta har kake ikirarin kai ne makusancin ta mutuniyar da ku ka birkitawa rayuwa har kuke tsammanin akwai wani lalen kati da za ku buga akanta kaico!". Ta kareshi da murmushin takaici a fuskarta kafin ta shiga nuna dakin da Mariya take kwance. "ko wannan ku ya kamata yaje ya tanaji duk wani kaya da ya sani ana jana'iza dashi domin shine kadai abin da ya kamata a daidai wannan lokaci Bala'in da kuka daurawa rayuwarta ya zama ajalinta..ko da yake dama ta fadi tun da dukkanku son ta kuke sai ku je ku dandatsata ko ya dauki ka sonsa". kuka ne ya kawo mata hari amma ta hana zuciyarta karaya ta hana idanuwanta zubda kwalla ta hana kanta yin rauni so take yi ta kwatarwa ƙawarta 'yancinta sai yau ta kara tabbatar da so bala'i ne so masifa ne sai yau ta kara tabbatarwa ba komai bane a cikin so sai tashin hankali duk wani kauɗi da ganɗoki da ake fadi da kambawa so na dashi na kayan jindadi da kwanciyar hankali ta karyata a so in dai haka so yake to gwanda ta zauna batayi aure ba in har sai anyi soyayya za ayi aure. numfashi take ajjewa idanuwanta izuwa lokacin sun gama cika da kwalla jingina tayi da bango tana zamewa har ta zube a kasa kamar wata kayan wanki nishi take yi so take yi hawaye su zo mata amma ina zuciyarta taki aminta mata wani zafi da raɗaɗi take ji tausayin Mariya yana kara ratsa jinin jikinta sosai take ji a jikinta in har mutuwar Mariya ya tabbata to ita kam ba zata taba yarda tayi so da wani ba domin ta tabbata SO AJALI ne ba komai ba. "Bata mutu ba". Runtse idanuwa tayi jin sautin kalmomin da suke ansa kuwwa a kunnuwanta ji take yi kamar a mafarki ji take yi kamar kalmar ta fito ne don kar ta sanya wa kanta abin da zai nakasta mata rayuwa laɓɓanta duka ta tura cikin bakinta tana cizawa zafin da taji ne ya sanyata buɗewa idanuwanta da saurin abin da ta ganine ya sanyata mikewa da hanzari. Dr.Karami, Dr.Aqeel,Huzaif gabadaya taga sun cikwuikuye likita kamar zasu raba shi gida Uku. Wani murmushi ne mai tafe da hawaye ya kufce mata kamar wata zautacciya haka ta tunkaro inda suke sai faman jinjiga shi suke 'wai ya tabbatar musu da gaskiya' duk kansu ta shiga duba da mamaki gami da wani irin farinciki mai girma gaske hadiye miyau tayi mai tauri kafin ta shiga nuna shi likitan da yatsa tana kuma nuna dakin da Mariya take. "Are You Sure?". gyaɗa mata kai yayi runtse idanu tayi. "Yaa Allah...wayyo Allah na me ma ya dace nayi..yawwa....likita kasan mi...kawai mu je na ganta...please". Ta hade hannayenta bayan ta gama rawar baki wajan furta kalaman rokon ja da baya yayi domin kwace kasan daga rikon da firgitattun mazajen har uku sukayi masa sai faman ajiyar numfashi yake yi. "Sosai take cikin matsala ba zan boye muku ba zuciyar tace ta kusan bugawa saboda tsananin damuwa da tashin hankali da take ci ban san mai yasa a kananun shekarunta ba ta fuskancin wannan matsalar har haka sosai naji tsoron yanayin da na ganta bani da tabbacin a halin da ake ciki a yanzu yarda zata farfado numfashinta dai yana harbawa nayi irin kokarina yanzu dai tana bukatar hutu sosai kafun muga yarda Allah zai yi". Dukkansu ajiyar numfashi suka saki mai karfi gabadayansu har sai dashi likitan ya dube su da mamaki Baseera ce tayin hanzarin dubansa. "Please Doctor zamu iya zuwa muganta?". Dubanta yayi kafin ya dube su Dr.Karami ya girgiza kai. "A,a wannan ta'addacin da naga anayi a nan in kuka shiga tayar mata da hankali zakuyi har abin da ake gudu ya afku". Yanayin da yayi maganar a dake ya sanya su zuba masa idanu suna kallon ikon Allah juyawa yayi ya koma cikin dakin kafun cikin mintina ya fito ya kama gabansa ba tare da yace da su komai ba. Nan suka shiga kai komo a tsakaninsu Baseera kuwa sai kwaɓa take yi da tsaki kamar zata tsinke harshenta tana faman zabga musu harara kamar idanuwanta za su fado kasa lokaci-lokaci take isa kofar dakin tana lekewa amma bata hango komai dalilin labulan da yayi wa kofar shamaki. Cikin wannan yanayin suka ji sautin takun takalma akan tayal din da yake malale cikin asibitin dukkansu suka jiyo jin sautin wajensu yake tunkarowa gabadayan su sakin baki sukayi musamman Huzaif da yayi fakare da idanu kamar wani gaula Hafsat ce take taku cike da isa da yanga sai faman taunar cingam take yi kamar wata Magajiyar karuwai daidai inda Huzaif yake tsaye ta tsaya ita ma ta karewa su Dr.Karami kallo kafin ta dubi Baseera da ita mata ta kalle ta ta watsar cikin nuna ban san ma Allah yayi halittar mai kama dake a nan ba hakan yayi wa Hafsat zafi domin dama can basa jituwa sam! a tsakaninsu duban Huzaif tayi wanda shima ita yake duba gabadaya jikinsa yayi la'asar sosai sai faman gyaɗa kai yake yi kamar wanda aka kama da laifin da bashi ya aikata ba. Dage laɓenta na sama tayi kamar wacce taci karo da kashi tana wani dakune hanci kafun ta hura cingum din bakinta tayi katon kwai ta fasa masa a fuska. "ban san mi yasa in ana gayyar tsiya nake ganin ka ba ban san min da yake sanyawa kake gangancin shiga ciki ba kai gabadayanka ba ka hada hanya da tsiya ba amma in ka ganta jikinka har wani ɓari yake yi kamar tsoho ya samu danyen jini budurwa danya sharaf a daren farko". Gyaɗa kai yayi cikin rashin abincewa Dr.Karami jin abin da Hafsat take fadi sai abin yayi matukar bashi mamaki ba yau bane farkon haduwarsa da ita da kuma yarda take rashin kunyarta amma yau yayi matukar mamaki da yanayin da ta nuna musamman ganin halin-ko-in-kula da ta nuna akan 'yar uwarta Mariya da halin da take ciki wani yawu mai tauri ya hadiye kafun ya kau da kai cikin kunar zuci. "Ban san mai yasa kake wahalar da kanka a inda ba a yin ka ba ance ba a sonka an tsaneka amma kaki daukar zuciyarka kayi nisa da inda ba ayi da kai haba sai kace mai MATACCIYAR ZUCIYA wanda ya yada kare ya dauke ya cinye tas!". Kuri yayi mata da ido ba tare da yace komai ba kuma da alamun bashi da niyar cewa din. Murmushi tayi na wulakanci kafun ta dora da cewa tana nuna shi da dan yatsa. "Wai kai ma so kake yiwa biyayya ko? ka biyo wannan zugar ta mara sa zuciya kai ma ka yaɗa hajar son ka ko za a saya kaico!". "ni ban san wata ƙaddara bace ta sanar dake ki dauko shanyayyun kafafuwanki ki zo wajan nan ba in ban da rashin zuciya da rashin aikin yi me ye naki a ciki ko akwai wani wanda kuke alaƙar mutunci dashi ne a nan da kika zo?". Baseera ta fadi cikin takaicin kalaman da Hafsat din ta fadi dubanta tayi shekeke kamar taga kashi "Ke kuma a soyuwa zaki sako min kazamin bakin ki mai dan banzan wari". "Ke dalla rufewa mutane baki yan fashi da makami kawai ke ko kunya baki ji ba ko da yake dama ba a gaje ta ba shiyasa tunda ba aji kunyar kwacen saurayi ba ai ba za aji kunyar biyo saurayi ba". Baseera ta sake fadi tana kau da kai daga kallon Hafsat da ta gama cika da bakin ciki da kalaman Baseera din duban Huzaif tayi wanda gabadaya kallo daya zakayi masa kasan yana cikin rashin hayyaci da kwanciyar hankali tsaki tayi rai a bace ta wurga masa wani kallo kafin ta juya cikin sassarfa ta bar wajan. Ba wanda ya bi ta kanta nan suka ji gaba da jajen zuciyoyinsu har zuwa wani lokaci mai tsayi da ya kwasar musu awanni uku cir!. Sannan likita ya sake zuwa zuwan nasa da ya kasance na biyar kenan yana dubata ba tare da ya bari sun shiga ba tausayin su yaji matuka da yanayin da ya gan su a ciki hakan ya ba su damar zuwa ganinta amma a bisa sharaɗin ba wanda zai yi ko da magana ne ta a zo a gani hakan suka yarda suka shiga yarda take haka take sai Oxgyen da yake taimakawa numfashinta yana kai kawo kirjinta na faman dagawa kamar zai faso waje sosai suka tsorata da yanayin da suka ganta don Baseera sai da ta toshe bakinta kuka ne ya kusan kufce mata kallon Mariya take cikin tausayi wacce lokaci daya duk ta zube dama yaya lafiyar kura balle kuma ta balle da gudawa duk fuskarta faɗa sai kwarmin idanu ruwan da aka saka mata sai faman tafiya yake yi Dr.Karami ne ya isa gareta idanuwansa na zagayawa a kanta da wani irin yanayi na rauni da tausayi gami da matsanancin so kau da kai yayi jin zuciyarsa na tsalle kamar zata faso kirjinsa ta fito gaban na'urar da take nuni da yanayin tafiyar numfashinta ya isa ya shiga kallo na dan lokaci yana faman ajiyar zuciya kafin likitan ya shiga yi musu bayani akan komai da yake afkuwa da ita na damuwa da kuma bugawa da zuciyarta take kokarin yi sharuɗa ya kafa musu sosai akan matsa mata da ake yi da kuma sanya mata damuwa da sanyata gaba ana mata rigimar da zata firgita mata zuciya sosai suka anshi sharuɗar kafun ya ba su dama kowanne yayi waje Baseera da Dr.Aqeel da Huzaif ne suka tafi gida amma shi Dr.Karami ya zauna akanta a matsayin wanda zai kula da ita duk wani abun da za a bukata duk da likitan yace ba sa bukatar mai kulawa daga wajan majinyaci amma ya ki yarda akan haka dole likitan ya kyaleshi bayan yayi masa ikirarin shima likita ne... *_Makaranta na masoyana na wannan labarin ina so a daidai wannan gabar kuma daidai wannan shafin ina bukatar gyara da kuma shawara sannan kusa ni tafiya ba tsokacin makaranta sosai take taba wani sashi na tafiyar zuciyar marubuci ya ji ba dadi don Alalh kuyi min tsokaci ta hanyar sako ko ta whatsapp domin raayoyinkun na da amfani sosai a gareni ga lambata nan ta whatsapp ina tsumayenku a ko ina kuke masoyana ina son ku so na sosai da sosai❤ 08076708191_* [9/14, 4:59 PM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA ARBA'IN DA BIYU. Sunkoyawa yayi da zubar debo ruwa a gorarsa har ya nitsar da ita sosai yana kokarin dagowa yaji ta maƙale gabadaya taki daguwa hakan yayi matukar daure masa kai shiru yayi kamar mai tunani wani abu kafin ya sake dago gorar tasa amma ina! sai yaji kamar an kara daura mata gingimeman dutse. "Ja'e zo ka taya ni gorata ta ki hidduwa daga ruwa". Ja'e dake tsaye yana gabzar danyen Mangwaro ya juyo ya dube shi kafin yace. "Ban fahimce ka ba me kake nufi?". "Zo ka gani mana don Allah". Ba tare da ya sake cewa komai ba ya tako zuwa wajen ya dube shi sannan ya dubi gorar da tayi kasa amma ga bakinta nan. "Jayota mana kai ma sai kace wani sakakke ya za ayi gora ta makale a ruwa?". Sake janyota yayi amma ina taki daguwa da karfin gaske ya fizgota gabadaya yayi baya ya zube a kasa gorar tayo waje sagale da ruwan rigar mutum hadi da kansa duk sunyo waje Ja'e dake tsaye bai san lokaci da ya kwala ihu ba ya ari na kare ya falle kamar wani zomo da yan farauta suka biyo shi Iro da ya baje cikin ciyayi mai taɓo ganin abin da Ja'e yayi ya tabbatar masa akwai abin da ya gani shima cikin tsorata da firgice ya k'urma da gudu shima ko tsayawa ganin abin da ke faruwa bai yi ba gudu ya shiga yi da yake irin siraran mutanan nan ne marasa jiki ga tsayi nan da nan ya kamo Ja'e da ke ta fama haki kamar wanda ya ɓalle daga lahira ya fado duniya. Ba su tsaya tambayar juna ba suka sake arcewa gudu sukayi sosai har sai da suka fara hango bunkokin rugar su kafin su tsagaita suna mai da numfashi Ja'e ya sunkoya riƙe da kafafuwansa yana duban Iro da yake gabansa. "Aradun Allah Iro lahira na hango". Ya fadi yana mai waige-waige cikin tsananin firgici da razana Iro da yake can nesa dashi ya dube shi cikin rashin fahimta. "Ban gane ba kaifa baka da hankali wa yace maka ana hango lahira daga nan duniya". Nishi Ja'e ya saki na wahala kafin ya tashi tsaye sosai ya dubi bayansa sa'an nan yace. "mutum ne fa kamar gawa na gani rike da Gorar...wai hala kai baka gani bane?". Iro da yayi shiru yana sauraron Ja'e jin abin da yace ya sanya shi ware idanu waje. "Aradu ban gani ba kawai biyo ka nayi don na tabbata abin da ka gani bala'i n...". A guje suka sake kwasa suna zunduma ihu kamar wasu zararru sai faman tsalle-tsalle suke kawai don sun ji motsi abu cikin ciyayin da suke kusa da ita da wannan yanayin suka karasa cikin rugar ihun da suke ya firgita mutanan cikinta nan da nan kowa ya shiga kallon su ana tambayar dalili amma ba wanda yayi kokarin tsayawa balle ya basu ansar abin da ya jefa su cikin firgicin da suka samu kan su. Da yake rugar ba mai girma bace kallo daya zakayi mata ka gane ZURI'A DAYA ce ta hadu a wajan don bunkokin na su tsilli tsilli suke a lissafe ba za su haura goma ba. "Iro wai kalau kuke kuwa? Wannan wani irin wauta ne da girman ku da komai amma kuna wannan shiriritar". Tsohon da suka gilma gindin wata bunka ya shiga fadin haka cikin yanayi na jin haushin abin da ya ga sunayi don mafiyawancin lokaci haka suke indai suka dawo kiwo sun dinga nuna yarintar su ke bayan kuma a shekaru ba wanda bai haura ashirin ba kuma ko wanne da matarsa ta aure. Ba su bi ta kan sa ba sai da suka karasa shiga cikin jerin bunkokin da suke kafun kowa ya faɗa bunkarsa cikin halin firgici nan da nan matan da suke wajan su ma suka tashi suna kokarin kwasa da gudu amma tsohon nan ya hana su . "Mariye jurɗe don Allah karku biyewa shiriritar su Iro kun san dai halin su ba sai na fada muku ba indai daukar hakki ne sun iya shi wajan tayar da hankalin mutane". Cak! Suka tsaya suna duban sa zuciyoyinsu na harbawa domin sun tsorata da yanayin da suka ga su iron. "Amma Baffa kamar wannan yanayin da suka shigo dashi ya bambanta da sauran lokuta alamu ya nuna kamar akwai dai abin dake faruwa". Gyaɗa kai yayi yana murmushi kafun ya gyara tsayuwar malfarsa akai yana duban surukan nasa "Nikam zan ga ranar da za ku daina daukar lamarin su Ja'e...". Ihun da suka ji an kurma ne gabadayan su suka juya da sauri suna duban Bunkar Ja'e Asiya ce ta yo waje a guje kai ko dan kwali babu zani na kokarin kwance mata sai faman mazurai take gabadaya ta firgice. Jurɗe ce tayi sauri isa gareta tana rukota sosai a hannunta ganin yanayinta da firgici. "Lafiyarki kuwa Asiya meke faruwa mai ya samu Ja'e?". Jikinta na mazari ta shiga nuna bunkar kafun taja numfashi mai karfin gaske. "wai gawa suka gano a bakin kogi". Ta ida tana mai kokarin rike zanin jikinta dake kokarin subuce mata. "Gawa!!!". Su ka fadi su duka cikin yanayi na zaro idanuwa waje Baffa da ke tsaye tun dazu da sauri ya kwaɗawa Ja'e kira yana tunkarar bunkar cikin hanzari. Ja'e dake makale cikin bunka sai faman mazurai yake yi jin muryar Baffa ya sanya shi takowa a hankali kamar wanda aka ce gawar tana biye dashi sai da ya leko kafun ya fito wani kallo Baffa yayi masa kafun ya dube shi sosai. "Wai shin me ke faruwa ne naji matarka tace wai gawa kuka gano bakin kogi ya abin yake ne ina shi Iron yake?". Cikin yanayi na firgici Ja'e ya hadiye numfashi mai tauri kafun ya dubi Baffan nashi. "Aradun Allah Baffa Gawa ce Iro yaje debo ruwa a garo kawai sai ya ganta". Cikin rashin fahimta Baffa ke duban sa kafun ya kwalawa Iro kira cikin hanzari ya fito shima yana faman mazurai har yafi Ja'e firgici ya tako ya iso matarsa na biye dashi sosai da sosai Baffa ke dubansa cikin yanayi na nazarinsa kafun yace. "Ina jin ka me ya firgita ku?". Rarraba idanu ya shiga yi kamar mai tsoron yayi magana gawar ta riko shi numfashi yake ja a hankali kafun ya dauke gumin da ya tsattsafo masa a goshi. "Baffa gawa ce na gano bakin kogi naje debo ruwa to shine gorar tawa ta makale nayi-nayi ta fito amma takiya sai da nayi daƙyar sannan na jayo ta a nan ne sai ga gawar mutum ta biyo gorara". "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un!". Gabadaya suka dauki salallami suna duban Iro da yayi firgai-firgai kamar wanda suka karawa firgici Baffa yayi ajiyar numfashi mai kwari cikin rashin aminta da zancen domin shi dai ba ya ganin wannan lamarin zai tabbata tunda ba yarda za ayi ace a tsinci gawa a bakin kogi shi dai ya san tun da yake zaune a nan sama da shekaru ashirin kogin nan bai taba cin mutum ba balle yace gawar wani dan rugar tasa ce sake duban su yayi ganin har yanzu suna cikin firgici ya sanya shi nazarin son zuwa ya je ya gani domin tabbatarwa idanunsa abin da ke faruwa numfashi ya sake ajjewa kafun yace. "Mu je na gano ni dai zuciyata ba ta gasgata maganar taku ba bana tunanin haka zata faruwa domin tunda nake ban taba ganin kogin nan yaci mutum ba amma dai..." Sai yayi shiru yana nazarin wani abu kafun ya sake dubansu yana mai cewa su je amma cikin su ba wanda ya motsa sai mazurai suke da mamaki yake kallon su ganin ba wanda ya motsa balle yace dashi wani abu. "Magana nake yi daku fa cewa nayi muje ku nuna min ko?". Nan ma ba wanda ya motsa sai dakuna fuska suke yi kamar za su fashe da kuka kamar wanda ba mazaje ba sosai Baffa ke mamakin halayensu na tsoro tun da yake haihuwa bai taba haihuwa 'ya'ya maza masu bakin tsoro kamar su ba ko don suna tsakiyar mata ne oho! shi wani lokacin abin mamaki yake bashi sannan kuma ya bashi takaici musamman in yayi lakari da har iyali suka ajje amma yarinta bata bar su ba. Tsuke fuska yayi cikin yanayi na rashin wasa muryarsa da sauti mai nuna bacin rai ya shiga nuna su da hannu. "ku wuce muje tun kafin ranku ya baci bana son sakarci kun ji ko". duban juna sukayi kafin su ja jiki su fara tafiya wannan ya tura wannan wannan ma ya tura dan uwansa Baffa ya shiga bunkansa ya dauko sanda sannan ya sauya riga ya fito ya dubi surukan nasa dake tsaye cirko-cirko sannan ya juya ya tafi tun da suka fito daga sashin su yawancin matayen rugar suke bin su da kallo don sun tabbata ba lafiya tun da suka ga Baffa da kan sa. Tafiya suke yi kamar wanda ba sa son zuwa Baffa na biye da su da sun tsaya sai ya daka musu tsawa cikin wannan yanayin suka tunkari kogin zuciyoyinsu suka fara lugudan bugu suka fara tirjiya kamar dabbar da ba ta son zuwa inda za a kaita ganin da Baffa yayi ba su da niyyar karasawa sai ya raɓa su ya wuce yana mai watsa musu kallon na raina muku wayo. Tun daga nesa Baffa ya fara tsinkewa da lamarin hango abu da yayi bakin kogin ruwa sai wuce yake yi ta wajan amma ba alamun motsi bakinsa dauke da addu'o'in neman tsari ya tun kari wajan zuciyarsa na harbawa amma haka ya dake ya isa wajan ba karamin razana yayi ba sosai ganin mutum zube a kasa rabin sa a waje rabinsa a ruwa turkewa yayi daga nesa yayi nazarinsa sosai ya tabbatar da cewa 'eh' gawa ce dagaske domin ganin yarda fuskar ta kumbure sosai ba ma ka iya gane halintarsa ta asali da hanzari Baffa ya isa har zuwa lokacin zuciyarsa da bakinsa ba su daina karanto addu'o'i ba ya tsorata sosai tsoron da ya kusan sanya zuciyarsa firgici har ya fara shakkan zuwa wajan gawar domin bai san abin da ya faru da wannan mutumin ba bai san mai ya kashe shi ba sannan yana tsoron abin da zai je ya komo musamman a halin rayuwar da ake ciki na yanzu baka san hawa ba baka san sauka ba fada TARKO da zai kashe maka rayuwa shi kuwa ba zai so haka ba baya fatan rayuwarsa ta kare da tashin hankali wanda zai hana zuri'arsa samun nutsuwa suma sosai zuciyarsa take karanto masa shafi-shafi na matsalolin da zai iya fadawa amma duk da hakan zuciyar tasa ba tayi tasiri ba domin wani bangare na cikin ta yana kwadaita masa ribar TAIMAKO a rayuwa numfashi yaja mai karfi kafin ya hadiye wani yawu mai tauri ya juya ya dubi su Iro da suka kara yin nesa dashi suna hangensa daga nesa murmushi yayi duk da halin da yake ciki bai taba ganin matsorotar maza irin su ba. Sai da ya kwashe mintina masu dan dama kafun ya karasa wajan gawar ya durkusa yana karewa fuskar kallo mai cike da suma kallo daya yayi masa ya gane babban mutum ne zuciyarsa yaji ta bugu lokacin da fuskar mutum tayi masa gizo da wata fuska da ya taba sani duk da dai ya manta a ina ya san ta amma fuskar tana yi masa kamanceciniya a hankali ya sanya hannu yana jayo shi daga cikin ruwan gabansa na cigaba da bugawa sosai gefen kogin ya ajje shi yana kare masa kallo zuciyarsa na ta nazarinsa kafun ya mike cikin yanayi na JARUMTA ya dubi su Iro da suka kara matsawa can nesa tun lokacin da suka ga ya fara kokarin fiddo da gawar da hannu yayi musu alamu su zo amma ba wanda ya motsa ganin in ya biye musu ba abin da zai yi hakan ya sanyashi takawa ya isa garesu. "kuje ku taho mani da amalanken shanu yanzun nan ina jiran ku". Duban sa sukayi cin rashin fahimta kafun Iro ya motsa laɓɓansa a dan tsora ce. "Baffa Amma...". Hannu ya daga masa cikin alamun yayi shiru. "kuyi abin da nace muku kawai bana son jin komai". Yanayin da yayi maganar rai bace ya sanya su jan jiki suka bar wajan da sauri domin yin abin da ya umurce su. Nan ya tsaya yayi shiru abubuwa da yawa suna masa yawo akai zuciyarsa sai kai komo take yi akan lamarin nan sosai da sosai abin ya daure masa kai bai san yarda zai kwatanta lamarin ba bai san ya zai dauke shi a zuciyarsa ba sosai yake jin wani iri a jikinsa abin da bai taba faruwa dashi ba tun da yake a rugar nan tashi sama da shekaru ashirin kenan amma abun ya zo masa kamar almara numfashi yaja kafun ya ɗaga kai ya dubi gawar daga inda take kwance mamaki al'ajabi duk sun baibaye zuciyarsa. Bai san me duniyar nan take so ta zama ba, bai san ya zamanin nan yake so ya zama ba, bai san me al'ummar nan ta wannan karnin suke so su zama ba, sosai yake tsoron duniyar nan a wannan zamanin sosai al'ummar cikinta suke firgita shi komai ya sauya tashin hankali an mai dashi kamar abin ado kisan kai abu mai sauki a yanzu kamar ran kiyashi zuciyarsa kuka take yi sosai in ya tuna al'ummar nan yarda suka ɓace a wannan zamani zai iya yuwuwa wannan bawan Allah kashe shi akayi ba tare da laifin sa ba kila yana da iyali a yanzu haka Allah kadai ya san matakin da suka kai na tashin hankali haka rayuwarsu zata dauwama kullum zuciyarsu na kuka tana kunci na rashin tabbacin inda yake... Karar amalanken da yaji ne ya katse masa dogon tunanin da ya faɗa da sauri ya juya ya dube su sannan ya nisa. "Meye yasa kuke abu ne kamar ba masu hankali ba, mai yasa kuke abu ne kamar ba 'ya'yan musulmai ba, mai yasa kuke abu ne kamar ba masu imani ba, mai yasa kuke abu kamar ba masu tausayi ba, mai yasa kuke gudun dan'uwan ku, ban san dalili ba? ko shakka bana yi duk da dai ban san waye wannan mutumin ba amma na tabbata yana da alaka da addinin musulunci ko ba ku da dangantakar komai da za ku iya taimakonsa dashi ya kamata ku dubi dangantakar addinin da kuka hada dashi shin ba kwa tunanin irin wannan lamarin ya faru da ku ko wani naku shin ba kwa tunanin ku faɗa halin rayuwa irin haka shin za ku so a bar ku cikin irin wannan mawuyacin halin ko wani dan uwa naku ya kamata ku sani duk zuciyar da bata taimako sannan bata tausayi to bata cika mai imani ba ya kamata ku sani shi wannan bawan ba shi ya saka kansa cikin wannan halin ba ina mai gargadin ku ku fidda tsoro a zuciyarku ku ajje komai na sakarci ku dauki hankali da natsuwa ku daurawa kan ku fisabillalahi yanzu in aka bar wannan mutumin a haka me kuke tsammanin zai faru dashi a amtsayin na matacce amma ba ayi masa suttura ba dabbobi ne da tsintsaye za su zo fa suna cin namansa wanda ba haka aka so ba ku kan ku na sani nan da dan wani lokaci in dai yana nan wajan wallahi ba za ku iya zuwa ba a yanzun ma kuna tsoronsa a haka ina ga kuma suffarsa ta fara canzawa ya kamata ku canza rayuwarku ku da zuciyoyinku tun wuri!". Shiru sukayi suna jin abinda Baffa ke fadi lokaci guda jikkunansu sukayi sanyi zuciyoyinsu suka mika su wani mataki na daban wanda ba su san suna dashi ba sosai suka ji wani yanayi mai girma ya dalsu a zuciyoyin su tsoro da fargaba ya shige su sosai dangane da maganganun Baffa sai faman rauyasa kai suke bai ce da su komai ba ya fara kokarin karkata akalan amalaken yana kora shanayen ganin haka ya sanya su sauri zuwa suka anshe shi duban su yayi kafun ya kau da kai sosai yaji dadi a zuciyarsa ganin maganganunsa sun yi tasiri a garesu a hankali ya fara takawa suna biye dashi har suka isa wajan gawar hannu ya saka yana kokarin daukarsa duk da a zuciyarsa yana ji ba zai iya shi kadai ba amma bai so yayi musu magana so yake yi ya ga halin da suke ciki sannan da yanayin da suka shiga a game da maganar tasa bai gama tunaninsa ba yaji su a kusa dashi a tsaye suna faman bin gawar da kallo sannan suna bin shi shima da kallo kafun su saka hannu duk da zuciyoyinsu suna harbawa amma duk da hakan sai da suka raruma jarumta suka sakawa kansu suka taimaka suka saka gawar a amalanken kafun suka hawan suka fara kokarin kaɗa shanun amma ya tsayen dasu isa yayi wajan wata bishiyar dogon yaro ya sanya hannu ya katso reshe mai girma da yake bishiyar ba tsayi gareta ba sosai kuma shi dama mai tsayi ne zuwa yayi ya lullube gawar dashi kafun ya hau su ja su tafi zuciyar sa cike da tausayi da jin ƙai ga wannan gawar abubuwa sosai yaji suna yawo akansa da zuciyarsa. A wannan yanayin suka shiga cikin rugar duk aka shiga bin su da kallo cike da yanayi na dan firgici a daidai saitin bunkarsa suka tsaya su Mariye duk sun fito daga bunkokin su sun yi tsarko-tsarko sai faman mazurai suke yi kamar wanda za ace musu kes! su kwasa da gudu. "Taimaka mu shigar dashi daga ciki ko". Ya fadi yana duban Iro da yake duban Baffa tun dazu yana son sanin abin da za ayi sun dauko gawa sun kawo gida bai san kuma abin da za ayi yanzu ba numfashi ya ja kafun ya dubi Ja'e sannan suka kama ba tare da sun buɗe gawar ba suka tattara har ganyen suka yi cikin Bunkar dashi ajje shi sukayi kan tabarmar dake shimfiɗe a tsakar bunkar duk suka saki ajiyar numfashi kafun Iro ya sake numfasawa a karo na biyu. "Baffa yanzu me za ayi masa to?". Murmushi yayi kafun ya shafa kasumbar fuskarsa wacce ta fara zama fara fat!. "Kokari zamu yi mu yi masa suttura mu kai shiga gidan sa na gaskiya shi kadai ne gatar da za muyi masa". Gyaɗa kai sukayi dukkannin su suna masu sakin ajiyar numfashi mai girman gaske. "Amma Baffa kana ganin haka ya dace ba fa mu san shi ba, ba mu san daga ina yake ba kana ganin in muka yi haka ba wata matsalar?". "Ja'e kenan yanzu ya kake so muyi in ba mu yi masa gatar kai shi gidansa ba in muka ce sai mun binciko wanene kasan lokacin da zamu dauka ba fa RAI gareshi ba, ba ma wannan ba yanzu in muka ce sai mun binciko yan uwansa ta ina zamu fara ba da wani haske ko tsani da za mu bi ya kai mu matakin da muke so lalube kawai muke a duhu hanya daya ce kawai muyi masaa suttura duk da dai ba mu san alkiblar da yake ba amma a zuciyata nayi amanna musulmi ne". Da mamaki suka dube shi. "Baffa kai ma dai da wata magana kake ai da ka kalli wannan zaka gane musulmi ne duk da dai ba a fuska ake rubutawa ba amma yanayin suffar mutum ma Allah na nuna yanayin sa da kuma zaton da za ayi masa na alkiblar da yake kalla". Ficewa sukayi gabadayan su waje suka tadda matan rugar da tsirarin maza sun yi dandazo suna jiran fitowar su Baffa kallon su kawai yayi lokacin da ya fito ya san za ayi haka dama dole su ne mi ba'asi ta yarda suka ga an shigo da mutum wanda suka tabbatar ba kalau ba kuma suka ga sabon abu da ba a tabayi a rugar ba. Cikin son fitar da su daga kokwanto nan Baffa ya shiga sanar da su abin dake faruwa ba karamar razana da tsoro suka nuna ba musamman matan masu tausayi wasu har da hawaye nan dai ya ja mazajen cikin su gefe duk da yawancin sauran sun fita kiwo ba sa nan musamman manyan 'ya'yan Baffa. Nan dai suka ba shi goyan bayan akan shawarar da ya yanke nan cikin kankanin lokaci ka shiga kokarin suttur tashi Baffa da kan sa ya shiga yi masa wanka cikin wannan yanayin wani al'amari ya so daurewa Baffa kai koma yace ya daure masa ya sanya shi tsayawa akan abun da yake yi domin ya lura cikin gawar na dan motsawa kadan-kadan alamun numfashi da farko bai yarda ba ya dauka juyawar da yake yi masa na wakan yake motsa cikin nashi amma sai yaga akasin haka da sauri ya mai da komai gefe ya ajje yana kallon sarautar Allah. Abu kamar wasa cikin hukuncin Allah sai ga motsin ya cigaba dayi har hannyensa sun fara motsawa nan da nan Baffa ya fita ya kira su Ja'e ya nuna musu abin da ke faruwa sosai suka nuna tu'ajibinsu. "Baffa ko dai yana da rai ne bai mutu ba?". Cewar Ja'e. "Akwai alamun ran a jikin sa kasan mi yanzun kamata yayi mu taimaka masa tunda alamun ya nuna da ransa". Cikin hanzari Ja'e ya mike yana duban Baffa. "Bari na kira Malam Jaura Mai Magani Baffa". Ba tare da ya jira ansar su ba ya fice jikinsa na ɓari dama ya matsu ya bar dakin domin gani yake kamar FATALWA ce ba wai sahihin mutum bane ya farko. Ya jima kafin ya dawo tare da Malam Jauro din irin mutanan nan ne masu maganin gargaji na kauye kafaɗarsa rataye da jaka ta fata kallo daya zakayi masa kasan ya tsufa sosai fuskarsa duk ta tattare abin ka da bafulatanin mutum ba kauri sai tsawo ga wani gemu da ya ajje yayi masa tsiri a haɓa yayi fari tas! dashi. Taimkon gangawa ya fara yi masa magani ya hada na sauyoyi ya murtsuke su kafun ya tsiyayi ruwan ya baiwa Baffa ya dura masa duk da izuwa wannan lokacin jikin nasa ya daina motsi hannu Baffa na k'yarma ya kai maganin saitin bakin sa yana mai furta Addu'ar neman dacewa ya shiga dura masa amma hakoran sunki buɗewa sai zubewa maganin yake yi a jikinsa ajjewa yayi gefe kafun ya sanya hannu ya buɗe bakin sosai wanda ya kunbure sosai jini duk ya taru masa laɓɓan nasa sun canza kala sunyi bakinkirin alamun mataccen jini a hankali yake dura masa wani na zubewa wani na wuce har ya gama ya mikewa Malam Jauro kokwan yana mai ajiyar numfashi kusan awa guda ana abu daya amma ko motsi bai sake yi ba amma Malam Jauro ya tabbatar musu da cewa yana da rai in Allah ya yarda zai tashi nan ya basu magunguna wanda za a dunga shafa masa da wanda za a dinga bashi na tsawon lokacin da zai farka domin ba karamar jika yayi ba jikinsa duk a kunbure yake ta ko ina sosai da sosai rigar jikinsa Baffa yayi kokarin cewa wacce gabadaya ta gama rine da jini. Sosai Babba ya tsorata lokacin da ya gama cire masa rigar dak'yar wacce sai da ya yage ta ba dai ya fidda ita ta wuya ba saboda mannewa da tayi da ciwon dake jikin nasa hannunsa na dama da ya kumbura ya suntume Baffa ya kurawa ido sosai yana nazarin sa kafin wani lokaci ya gane harbi akayi wanda ya same shi a hannun nan ya shiga kwaɓa wani magani wanda Malam Jauro ya bashi ya shafe masa wajan dashi kafun dukkannin su su fice daga cikin dakin zuciyoyinsu cike da fargaba da yanayin da suka gan maras lafiyar a cikin in ba don Malam Jauro yace akwai numfashi ba ba su yarda ba musamman Ja'e da Iro wanda sukayi zaton kawai dama can a mace yake ganewa ne ba suyi ba suke ganin kamar motsi yake yi duk da wani ɓari na zuciyoyin su na sanar da su da sauran numfashin sa. ****** "Anya Baffa wanna mutumin zai tashi kuwa?". Cewa Ja'e dake faman gasa masa jiki da tafasheshen ruwan magani wanda izuwa wannan lokacin jikin nasa ya sabe sannan kuma numfashin sa na fita a hankali. Baffa wanda ya kure shi da ido tun dazu yana kallonsa yau kwana biyu kenan zuciyarsa na damuwa da lamarin mara lafiyar nan da ya tsinta sosai ya damu sosai yake son ya ga ya tashi kan kafadun sa yana so ya san ko waye shi yana son ya san wani abu game dashi sosai yake ji a zuciyarsa wani lamari mai girma yana tattare da shi zuciyarsa da idanunwansa suna nazarin fuskarsa wanda har zuwa wannan lokaci bata dawo daidai ba ko idanun nasa bai iya buɗewa. Numfashi ya ja kafun ya dube Ja'e. "zan so ace ya tashi kan kafafuwan sa sosai nake bukatar haka ina so ya dawo duniyar nan ya cigaba da rayuwa sosai nake ji a jiki akwai wani al'amari da zai faru a game da wannan mutumin ko da dai ban san sa ba amma ina ji a jikina akwai wani abu a boye". Shiru yayi yana duban Baffa jin abin da yake cewa wai akwai wani abu da yake zaton zai faru anya kuwa meye zai sanya kansa damuwa akan mutumin da bai san shi ba bai san daga ina yake ba... Motsin shigowa haɗe da sallama da akayi ya tsinke musu zaren tunanin da suke yi Asiya ce ta shigo hannunta dauke da kwarya cike da damammiyar salala mai dauke da hadin magani a ciki durkusawa tayi har kasa. "Sannu Baffa gashi an gama". Ta fadi tana mai ajjewa gefe guda tana mikewa kan kafafuwanta bayan ta karewa mara lafiya kallo zuciyarta da tausayi sosai a ciki sannan ta fice tana mai dauke kwallar da suka kawo idanuwanta hari. "Baffa!" Ja'e ya fadi da sautin murya yana mai zaro idanuwa waje cikin yanayi na firgici da sauri Baffa ya dube shi kafun ya sauke idanuwansa kan maras lafiyar jini ne ke fitowa ta bakin sa bakikkirin kirjisa sai faman harbawa yake yi cikin sauri-sauri ko ina na jikinsa sai motsawa yake yi kamar wanda aka jonawa wayar nepa da hanzari Baffa ya mike ya isa wajansa yana dafeshi cikin yanayin fargaba ganin jinin sai bulbulowa yake yi yaki dainawa. "Maza Ja'e maza tashi ka kirawo Malam Jauro yi hanzari". Tun kafun ya rufe baki Ja'e ya fice daga gudu cikin kankanin lokaci suka iso a tare Malam Jauro na kallon abin dake faruwa bai wani damu ba ya dubi Baffa. "Ba wata matsala bace buguwar da yayi ne jini ya tarun masa shine yake amayar dashi hakan ma duk cikin samun sauki ne". "Haba Malam Jauro ya zaka ce haka ka ga mutum na aman jini amma kace ba komai anya kuwa". "Ni na fada maka ai in ka lura da jinin ai ba lafiyayye bane ya rigaya ya lalace ko ya tsaya masa a jiki ba abin da zai haifar masa sai wata matsalar cutar ka kwantar da hankalin ka in Allah ya yarda zai farko kuma cikin sauki". Ajiyar zuciya Baffa yayi mai girma kafun ya koma gefe yana sharce gumin dake ta faman tsantsafo masa a goshi. Jini sosai ya zubar kafun wani lokaci ya lafa nan Malam Jauro yayi masa yan daburansa kafun ya dura masa wani magani da ya ciro daga jakar sa sannan ya bukaci wani abu mai dan dumi mai ruwa-ruwa domin ya bashi nan take Baffa ya mika salalar da Asiya ta kawo sai da ya kare mata kallo kafun ya dubi Baffa. "Dama ba a bashi ba tun dazu da nace". "Yanzu aka gama ina kokarin bashi sai ga wannan lamarin ya afku" Ba tare da ya sake magana ba ya shiga dura masa salalar a hankali cikin ikon Allah ya buɗe baki ya mikawa cikinsa sakon abincin da yaji yana saukar masa amma duk da hakan idanuwansa a runtse suke ba su buɗe ba sai da ya sha sosai sannan Malam Jauro ya dubi Baffa. "In Allah ya yarda komai zai zo da sauki tun da hakan ta kasance yanzu dai ku bar shi zuwa wani lokaci muga yarda Allah zai yi". Gyaɗa kai sukayi suna yi masa godiya kafun ya mike ya sabi jaƙarsa ya fice daga bunkar. Haka su Baffa suka cigaba da jinyarsa a hankali yana samun lafiya jikinsa na komawa daidai sai dai magana ce ba ya iyayi sam! sannan idanuwansa sun buɗe sai dai mutane ma dishi-dishi yake gani a haka har sati guda ya shuɗe Baffa bai gajiya da taimaka masa ba shan maganinsa cin abinci har makewayi shi yake taimaka masa ya kai sa da kan sa daidai da rana daya bai gajiya ba da kansa yake za gayawa dashi cikin rugar domin motsa jiki shi ya zame masa DAN JAGORA lokaci lokaci yana tambayarsa waye shi? Amma ba ya bashi ansa sai dai idanuwansa suyi ta zubda hawaye yayi ta kokarin yin magana amma ba dama sai dai yayi ta jan numfashi a haka har suka saba da Baffa sosai da sosai mutanan gidan ma haka rugar gabadaya ba wanda bai san DAN MAKAHO ba sunan da suke kiransa dashi kenan ko DAN KURMA a haka ake ganewa amma ba sa fadi gaban Baffa domin fada yake yi sosai ya nuna bacin ran shi akan haka domin komai ya samu bawa na dadi da akasin sa DAGA ALLAH NE kuma tun fil'azal ALKALAMIN ƘADDARAR bawa ya rubuta hakan sai ta faru dashi a duniyarsa. Shakuwa sosai Baffa yayi dashi domin a zuciyarsa yana jin wani bakon yanayi game dashi lokaci lokaci yake jin gabansa na faduwa wanda ya rasa dalili musamman in yana kallon fuskarsa sai ta dinga yi masa gizo da wanda ya taba sani amma ya rasa tunanin da zai kara masa haske akan fuskar cikin wannan hali suka shafe wata guda izuwa lokacin idanuwansa sun buɗe sosai yana ganin kowa da kowa ranar da ya fara ganin fuskar Baffa ba karamin yanayi na fargaba ya shiga ba zuciyarsa ta shiga bugawa da sauri-sauri lokaci guda ya firgice sai mazurai yake yi ji yake kamar ya kwashi kafafuwarsa ya zura da gudu ko kuma ya nutse cikin kasa jikinsa sai ɓari yake yi Baffa dake gefensa yana ta faman bashi labarai sam bai lura da abin dake faruwa ba motsin mikewa da yaji yayi ne ya sanyashi dubansa ganin yanayi da yake ciki ya sanya shi mikewa ya riko masa hannu. "Lafiya me ke damunka?". Baffa ya fadi yana mai dunduba jikinsa kafun ya sauke idanuwansa a saitin nasa hakan ya kara fadar masa da gaba shi kansa Baffa ji yayi gabansa ya yanke ya fadi lokaci guda... *_KAMALA MINNA_*😘😘😘😘 [9/15, 9:28 AM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA ARBA'IN DA UKU. Sosai zuciyarta take bugawa a duk lokacin da Al'amarin Auranta da Dr.Erena ya zo mata filin tunaninta komai nata kwancewa yake yi komai nata take ji yana canzawa kamar ba nata ba. Ta rasa ya zatayi ta rasa mai ya kamata tayi zuciyarta na zafi zuciyarta na raɗaɗi raɗadi mai girman gaske kudirin zuciyarta kawai take hangowa da ta dauka akan wannan azzalumin mutumin bata so abin da zai hadata dashi a inuwa daya sam-sam ko zaman da take yi a Company sa kawai tana yi ne don cinmma burinta amma ga yarda lamarin ya kasance har ya kai ga zancen aure a tsakaninsu. Bata san wata irin rayuwa zatayi a gidansa ba bata san ya zata zauna ba zuciyarta na zafi tana shiga kunci duk lokacin da tunanin aurenta ya fado mata ba ta shirya masa ba ko da na kwana daya ne amma ba yarda za tayi tunda Hajiya Layla ta nuna kaunar ta akan lamarin kuma ta wannan hanyar ce kawai za su samu abin da suke so. Sosai take mamakin yarda Hajiya Layla ta dauki lamarin da girma ta bada lokacinta da komai da ta san zai taimaka wajan tafiyar da komai yarda ya kamata. "Areefa bawai ina son ki auri Dr.Erena bane a son raina a,a wallahi in da zan buɗe miki zuciyata ki ga bakinciki da takaicin da take yi akan wannan lamarin zaki ce naki ba komai bane amma na daure na mika zuciyata wani mataki na hakuri domin ganin ta yarje wannan lamarin ya kasance". "Maama ban san ya zan koyi zama da makiyina ba ban san ya zan koyi zama da mutum kamar Dr.Erena ba daidai na sakan daya ne wai da sunan a idanuwa daya a matsayin mata da miji". Wasu hawaye suka zubo mata a kunci masu dumi bata yi kokarin dauke su ba domin ko ta yi hakan ba daina zuba za suyi ba. Hajiya Layla ce ta saka hannu ta dauke mata tana mai kwantar da ita kan cinyarta. "Areefa ina so ki san wani abu guda san nan ki saka shi a zuciyarki auren Dr.Erena ba yana nufin kashe miki rayuwa bane auren Dr.Erena ba yana nufin numfashin ki ya daina wanzuwa bane a doron duniyar nan ki sani rayuwa ce zaki yi ta daukar fansa a gidansa wacce nake tsammani ita ce hanyar da tafi dacewa sannan ke dai ki zuba ido kiyi kallon komai zaki sha mamaki akwai ranar da zata zo da kan ki zaki zo kina bukatar al'amarin da yake wanzuwa a daidai wannan lokacin ba zan sanar dake komai yanzu ba amma duk ranar da komai ya tabbata zaki san komai". Tashi tayi tana duban Hajiya Layla cike da mamakin furucinta sai faman juya idanu take yi tana rausayar da kai tana kokarin yin magana wayarta ta dauki Ring juyawa tayi ta dubi wayar a cikin jakarta dake yashe tun da ta dawo aiki yau gabadaya ta kasa sukuni ta kasa zaune ta kasa tsaye Hajiya Layla ce ta kai hannu ta dauki jakar ta fiddo da wayar ta mika mata ba musu ta ansa ganin mai kiran ya sanyata saurin dagawa don dama kamar ya san ta na cigiyarsa don sun kwana biyu ba su hadu ba gabadaya ta shiga wani irin yanayi na tashin hankali musamman yarda Dr.Erena ya sako ta gaba akan ta bashi dama ya turo domin neman aurenta. Numfashi taja jin muryar Alhaji Abdulwahaaab ya ambaci sunanta. "Areefa ina kika shige kwana biyu ne?". Numfashi ta hadiye mai tauri kafin ta dubi Hajiya Layla. "kai dai kawai bari al'amarin duniyar nan ne yake neman sha mini kai wallahi akan maganar mutumin ka ne Dr.Erena". Murmushi yayi mai sauti wanda har sai da Areefa taji sosai kafun yaja numfashi. "kisan na kusan barin duniyar nan kuma ba wanda na daurawa sai Dr.Erena kisan an tare ni a hanya akayi min dukan tsiya har sai da na rasa kai na...". "What! Me kake cewa Alhaji Abdulwahaab duka fa kace Yaa Allah!". Ta fadi tana mikewa a razana lokaci guda ta ji kanta ya buga ta sanya hannu ta dafe shi sai numfashi take saki da sauri sauri kamar wacce tayi gudun ceton rai. "kenan sai da yayi abin da yace zai yi ko wai shin me ke damun wannan mutumin ne na lura gabadaya shi cinnaka ne bai san na gida ba". "Rabu dashi kin ji yanzu ya maganar ku ina kuka kwana akan batun auren naku don ya kamata ace kin ajje duk wata fargaba da tsoro a zuciyarki kin fuskance shi sosai ki yarda ki bashi hadin kai a yi aure nan wannan dama ce sosai a gareki da zaki cika burin ki gami da kudirinki". "bana tunanin zuciyata zata aminci bana tunanin zan ita zama da shi bana tunanin burina da KUDIRINA za su tabbata in dai ta hanyar aure ne tsakanina da Dr.Eren...". Fizge wayar taji anyi da sauri ta juya ganin Hajiya Layla taga fuskatar ta sauya da bacin rai ya tabbatar mata da bata so abin da take fadi ba. "Alhaji Abdulwahaab". Hajiya Layla ta fadi bayan ta daura wayar a kunnanta kafin ta nisa bayan ya ansa. "Karka damu da duk abin da take ce maka Alhaji Abdulwahaab zuciyar Areefa ban san abin da ke damun ta ba amma ka bar komai a hannu na ni dai taimakon da nake so kayi mani a wannan tafiyar a yanzu ka neman min mutanan da za su kasance a mtsayin iyayen Areefa ina son cikin watan nan bikin nan ya tabbata...". "Maama!!!".. Areefa ta fadi tana zaro idanu waje kamar wacce ta ga mugun abu wani kallo Hajiya Layla tayi mata tana sauraron abin da Alhaji Abdulwahaab yake sanar da ita akan komai zai gudana ba matsala sauke wayar tayi ta cillar da ita kan kujera kafun ta dubi Areefa. "ya kamata ki san wani abu guda daya lamarin nan fa sai ki ajje duk wata kiyayyer da kikewa Dr.Erena a gefe ke kin sani mutum ne dan duniya in har kika bada matsala wallahi tsaf zai kashe ki har ni da ma duk wanda ya san suna hada hannu damu don haka tun wuri ki san abin yi kuma ina so in kin fita aiki gobe ki sanar dashi kin aminci nan da sati guda ya turo". Baki ta saki tana kallonta cikin mamaki da takaici a zuciyarta komai take ji yana canza mata duniyar taji tana juya mata da tashin hankali mai girma wani ciwo taji mai girma zuciyarta na kara shiga kiyayyar Dr.Erena na daɗuwa girgiza kai ta shiga yi kafun ta yi hanyar dakinta da gudu tana sakin wani numfashi mai wahalar gaske. Wannan rana haka Areefa ta wuni cur! ba wani akayan farinciki har zuwa dare ko runtsawa ba tayi ba Hajiya Layla ta zo ta bata baki amma ina tashin hankalin da take ciki ya zarce a kwatantashi gabadaya a firgice take ba ta shirya ba bata da lokacin yin wannan aiki zuciyarta ba zata aminci ba. Haka tayi ta saƙe-saƙe har zuwa wani lokaci kafun wani barawon barci yayi gaba da ita a nan zube tsakar daki. ***** A sanyaye take shiryawa gabadaya jikinta ya mutu sosai take jin zuciyarta na mikata wani mataki mai girma gaske yana haifar mata da wasu lamaruka masu girma a zuciyarta numfashi take dak'yar ji take yi kamar wacce ake toshewa hanci da baki. Turo kofar da akayi ne ya sanyata hanzarin mikewa Hajiya Layla ce ta tokare bakin kofar tana binta da kallo kafun ta kau da kai. "Kisan karfe nawa yanzu kuwa Areefa? Wai mai yasa bakya jin magana ne Areefa ya kamata kiyi hanzarin shiryawa ki tafi aikin nan rashin zuwa aikin nan zai iya canza tunanin mutumin nan ta inda baki taba zato ba wallahi ke da kanki kwanaki kike bani labarin abinda wata ta zo tana gaya masa akan ki na cewa ba don Allah kike aiki a Company din sa ba akwai KUDIRI da kike dashi a zuciyarki ba ki tunanin wannan tunanin ya fara tasiri a zuciyarsa bakya tunanin in bakya nan ta sake zuwa ta sanar dashi har akai matakin da zai yarda yanzu ya dace ace kina nan nan dashi ya gane eh da gaske auran sa zakiyi sannan karki sake ya gano ko yar karamar hanyar da za ta bashi dama ne ya fahimci wani abu wallahi in baki iya kama barawo ba to tsaf! barawo zai ka maki Dr.Erena da kike gani ba karamin kwallon shege bane...ko dayake ba sai na fada miki ba ke kan ki kin san waye". Tana gama fadin haka ta juya da hanzari ta bar dakin ta bar Areefa tsaye tana kokarin sanya dankunne cak! ta tsaya tana jin maganganun Hajiya Layla nayi mata yawo akai tunanin faruwar wani abu daban da yarda zata kasance ya dire mata a zuciya tabbas ta sani dole wani abu ya faru in har tayi sake musamman yanayin da Mufeeda take kokarin sanya Dr.Erena ya so ta ta sani ko wani hali kuma komai zata iyayi don cin ma burinta. Cikin hanzari ta karasa saka dankunne ta saka takalmi kafun ta kara gyara fuskarta sosai da sosai ta dauki jakarta bayan ta duba kanta a MADUBI sa'annan ta fice daga cikin dakin bata samu kowa a falon ba hakan ya tabbatar mata Hajiya Layla na daki bata yi yinkurin zuwa gareta ba illa saurin ficewa da tayi. Tana shiga motarta ta fizgeta sosai tana zabga guda gabadaya kwanyarta ta mikata cikin wani yanayi a yanzu da take hango Mufeeda tare da Dr.Erena tana karantar dashi komai akan Areefa gabanta taji ya tsinke duk da dai ta tabbata Mufeeda ba za ta sake dawowa wajansa ba sannan kuma shima yana nuna rashin so akanta sosai. Da wannan tunanin ta isa Company din sai da ta tsaya bakin Get tayi kokarin saita numfashin ta kafun ta karasa ciki tayi Parking nan ma sai da ta dau mintina tana karewa motocin da suke zube a wajan kallo kafun ta dire a ta Dr.Erena wani numfashi ta ja mai tauri kafin ta buɗe motar ta fito a hankali ta shiga takawa kamar mai tausayin kasa har ta kai bakin kofar da zata shigar da ita cikin Reception din bayan sun gaisa da Security tana kokarin sanya kai ciki sai ga Dr Erena shima ya sanya kai zai fito saura kadan su yi gware da sauri taja da baya tana mai da numfashinta da take ji yana fizga runtse idanu tayi kafin ta buɗe su lokaci guda ta dube shi wanda shima gabadaya ya shagala da kallonta sai faman zabga murmushi yake yi sosai ta ji gabanta na bugawa kafun tayi kokarin kirkiro yaƙen dole tayi masa tana kokarin raɓashi ta wuce amma yarda ya tsare kofar ya sanya dole yin maganar da bata so yi ba. "Barka da safiya Sir". Ta fadi ba tare da ta dube shi ba bai ansa taba kuma da alamun bashi da niyyar ansa ta din sosai ta matsu ta bar wajan yarda take jin kafafuwanta na wani iri lauyewa kamar za su zubda ita a kasa sai da ya gama shan sharafin kallonta sannan ya kau da kai ya na mike mata wani abu dake hannunsa. "in kin shiga ki karasa min dashi cikin Office". Ya fadi ba alamun wasa sosai take kallonsa da abun da yake mika mata lamarin ya shiga tsingular mata zuciya wanda take kallo a matsayin raini eh mana raini ta yaya za ace mutumin ya fito da abu daga ciki sannan kuma ita da zata shiga yanzu ya bukaci ta mai da masa mai yasa ya fito dashi bata san abin da yake hawa kan Dr.Erena ba a yan kwanakin nan yana shige mata sosai ita kuma bata son haka ansa tayi sannan ta wuce ciki binta yayi da kallo yana sakin murmushi harda taɗɗar baki kamar namijin da ya shekara hamsin gidan yari ya fito ya ga mace kafun ya juya da sauri ya isa wajan motarsa ya bude abu ya dauko sannan ya rufe ya kama hanyar kowama cikin reception din. Ita kuwa Areefa tana shiga bangarenta ta isa ta ajje jakar da sauran tarkacenta kafun ta dubi abinda Dr.Erena ya bata ta shiga juya shi ba wani abu bane na azo a gani kawai neman shiga rayuwarta ne da hanzari tayi hanyar benan cikin sauri don bata so ya zo ya tadda ita a ciki don tasan kadan daga aikin sa ne. Tana hawa wajan Office dinsa ta tadda sakatariyarsa ko ta kanta bata bi ba ta karasa ta shiga Office din can wajan Table ta isa ta ajje masaa kafun ta juya tana karewa Office din kallo tana yatsine fuska sa'anna ta ja kafafuwan ta tana kokarin fita mutum ta gani tsaye bakin kofar harɗe da hannaye a kirjisa wani irin dokawa taji gabanta yayi kafun ta daure fuska tamau! "Ina zuwa ko". Ta fadi cikin rashin son kawo mata wasa murmushi yayi kafun ya tako kamar zai shige mata jiki hakan ya sanya ta saurin ja da baya. "Areefa ban san me zan miki ba kuma nayi iri bakin kokarina don ki bani dama amma kin kiya ban san dalili ba?". Ya fadi yana mai kare mata kallo kafun ya dora da cewa. "Ina so a yanzu ayi komai ya wuce don wallahi ba zaki fice daga Office din nan ba sai kin fada mini matsayata a gareki". Wani irin dokawa zuciyarta tayi amma bata bari hakan yayi tasiri a fuskarta ba kau da kai tayi. "Areefa ya kamata ki ce dani wani abu ki baiwa zuciyata dama ta so ki ta kauna ce ki ta daɗe tana daukon son ki amma ke kin ki yarjewa dagaske nake ba da wasa ko yau ki ka ce na fito akan zancen aure wallahi ko awa daya ba za a kara ba". Yaa fadi kamar wani karamin yaro sosai maganganunsa suka taba mata zuciya amma sai ta nuna halin ko in kula sai ma kokarin raɓashi ta wuce take yi amma yaki bata dama sun jima haka kafun ta yanke hukunci da taga yafi cancanata wanda take ganin illa ce mai girma gareta numfashi taja kafin ta saita kanta sosai ta dube shi. "Dr.Erena ni ban ki ta taka ba..ko da yake kawai abin da za ayi mu bari nan da sati daya lokacin na sanar a gida sai ka turo". Ta fadi ba a son ranta ba tana jin yarda zuciyarta ke yayyagewa da tashin hankali sosai taji jikinta na ansa bakon lamari mai girma da sauri ta rabashi ta wuce ganin ya saki baki yana kallonta kamar wani butum butumi. *_KAMALA MINNA_*😘😘😘😘 [9/15, 7:33 PM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA ARBA'IN DA HUDU. Sosai ta shiga tashin hankali cikin lokaci kankani ta rasa mai yake mata dadi a filin duniyar nan komai ya kara kwance mata tashin hankali ta ya kara hawa mataki mai girman gaske bata san me za tayi ba bata san mai ya kamata tayi ba lokaci tafiya yake komai kara kusantowa yake yi har zuwa wannan lokacin ta rasa mafitar da zata samu don cimma burin ta ba tare da auranta ya tabbata da Dr.Erena. Numfashi take ja cikin sauri-sauri tana faman juyi saman faɗaɗɗen gadon ta wanda take jin sa kamar kan garwashin wuta take kwance komai na duniyar take ji yana yi mata k'iwa baya son ta da farinciki ko yaya ne. Zuciyarta na ta hasaso mata cewa 'ta kashe shi ba tare da kowa ya sani ba' amma ta kasa tana tsoron haka ba kisa a tsarin daukar fansanta bata so ace wani abu ya gifta a tsakaninta da shi wanda zai sanya ta zama sanadin kashe shi tsoro take ji tsoron abin da zai je ya dawo tsoron yawan zunubansa da zai dawo kanta tana tsoron mutuwarta bata shirya ba ba zata iya ba. 'to ki kashe kanki tunda baki shirya auren dashi ba'. Zuciyarta ta sake bata wani zaɓin na daban wanda yayi matukar girgizata lokaci guda ta shiga girgiza kai kamar wanda ya fada mata maganar a gabanta yake ba zuciyarta ba wasu hawaye ne masu dumi taji sun zubo mata sosai take jin kunci da matsi cikin zuciyarta sosai take jin zuciyarta na mikata wani mataki mai tashin hankali sosai take jin zuciyarta na buɗe wani wagegen ciwo mai girman gaske. Runtse idanu tayi sosai tana jin yarda jijiyon kanta da na cikin idanuwanta ke wani irin murɗewa da tashin hankali tana jin yarda wani irin raɗaɗi da zafi ke samun mazukunni cikin idanuwanta mikewa tayi daga kwance da take tana buɗe idanuwan nata hannaye bibbiyo ta zabga tagumi tana kallon yanayin DUHUN DARE da ya mamaye cikin dakin bata ganin komai ko jikinta bata iya hangowa sake runtse idanu tayi kafin ta sauke kafafuwanta a gefen gadon tana kai hannunta wajan fitilar dake girke gefen gadon kunnawa tayi haske ya wanzu sosai ta ko ina dakin ta shiga bi da kallo kafun ta mike saman kafafuwanta da take jin su kamar za su watsar da ita zuciyarta na ta karanto mata huɗubobin da suke kara caza mata kwanya. Maganganunta da Alhaji Abdulwahaab ne suke dawo mata a jiya da rana inda yake kara karfafa mata gwuiwa amma tana zillewa. ***** "Ban san mai zan ce miki ba kuma Areefa da farko na dauko za ki zama jaruma mai dakakkiyar zuciya wajan cimma fata da burin da kike dashi a zuciyarki amma gabadaya duk wannan fatar da burin naki ya rugeje lokaci guda ban san mai yasa ba Areefa ban san mai yasa kike kaunar jinkiri a wannan lamarin ba dama ce sau daya take zuwa in kuwa ta kubuce da wuya WATA DAMAR ta sake zuwa". Cire hannayenta tayi daga tagumi tana mai runtse idanu kafun ta buɗe su sosai tana dubansa zuciyarta na kara narkewa da lamarin Aurenta da Dr.Erena. "ba wai na cire burin fata na bane akan Dr.Erena ba ba abin da ya canza...". Ta fadi dakyar tana jan numfashi kafun ta dauki Glass Cup mai dauke da sanyayyan ruwa ta kai bakinta ta kurba ba wai don jin dadi ba a,a domin kuwa ji take yi kamar ta kurbi maɗaci a dandanon da harshenta ya bata runtse idanu tayi ta hadiye shi dakyar kafun ta buɗe tana dubansa shima idanuwansa na kanta. "ina son fatana a kansa ya tabbata amma wannan lamarin da aka kawo min ne nake jin kamar zuciyata ba zata iya hakura ya tabbata ba". Mikewa yayi kan kafafuwansa yana binta da wani irin kallo kafun yayi taku kadan ya goya hannayensa a bayansa. "ko RIGAR SILIKI haka ta ganki ta barki Areefa ana taroki ta nan kina watse wa ta can ban san mai yasa ba...ko da yake shikenan amma ki sani auren ki da Dr.Erena shi ne mafita kuma ita ce hanyar da zaki bi domin cimma burinki kamar yarda Hajiya Layla ta fadi bana tunanin zata cutar dake ko da cikin rashin sani ne ki sani baki da wata a duniyar nan ita ce uwarki da ubanki baki da mai kaunarki kamar ita ba zata taba yin abin da zai taba miki rayuwa ba kuma kema kin san haka don haka ya kamata ke ma ki yaki ce duk wani k'i da zuciyarki take nuna miki ki koya mata hakuri da juriya". ***** Wani huci ta saki tana mai cusa hannayenta cikin gashin kanta zuciyarta taji tana sauya bugu da sauri-sauri a hankali ta zube kan gadon tana kwanciya gami da runtse idanu so take yi ta koyi hakuri da juriya domin ganin tabbatar wannan lamarin amma ta kasa amma ya zame mata dole ya zame mata tilas! Ta koyi jarumta da juriya a zuciyarta domin ganin komai ya tabbata yarda ya kamata tayi alkawarin yin abinda Maama take so a gareta da wannan tunanin barci barawo yayi awon gaba da ita ba ta farka ba sai wajan shidda da rabi shima Maama ce taji ta shiru ta shigo dakin sai da kare mata kallo cikin yanayin tausayawa domin daga ganin kwanciyar barcin bata yi shi tadadin rai ba kuma ba da wuri ba a hankali ta zauna kusa da ita ta shiga shafa mata goshi a hankali Areefa ta buɗe idanuwanta mai cike da barci ganin Maama ya sanya ta kara buɗe tana ya mutse fuska cikin muryar barci tace. "Maama!". Murmushi tayi mata kafun tace. "bakiyi barci da wuri ba ko Areefa kin sakawa kanki damuwa ko?". Girgiza kai tayi kafun ta mike zaune tana mai duban agogo ganin karfe bakwai saura ta ware idanu da sauri. "Yaa Allah har lokaci ya tafi haka". Tana kokarin mikewa Maama ta rike mata hannu ta koma ta zauna tana kallonta cikin rashin fahimta numfashi ta ka kafun tace. "Ba zan takura ki ba Areefa domim bana son abin da zai sanya ki a damuwa amma bari zan fada miki dalilina nayin haka din yanzu na san zakiyi amanna da batuna da nake jajircewa domin ya tabbata...". da sauri Areefa ta kai hannunta bakin Maama tana rufe fuskarta da wani irin yanayi. "kiyi hakuri Maama komai ya wuce na yarda komai ya tafi yarda da kike so zan baki hadin kai daga wannan lokaci bari ki gani daga yanzu ma". Ta mike da hanzari ta fada toilet wanka ta sallo kafun ta zo ta tsantsara kwalliya ta sanya riga da siket ta saka wanda suka dan kamata kadan takalmi mai tsini ta saka gami da dauko wata gold-bag mai shegen kyau ta daura glass no respect sosai ta fito kyanta yakara bayyana kamar ba wani abu da ke dawainiya da ita sai murmushi take zabgawa Maama ita kuwa baki ta saki tana kallon ikon Allah kafun ta mike kan kafafuwanta ta riko Areefa ta rungumeta sosai da sosai sannan ta sake ba tare da tace mata komai ba sosai take dubanta bayan ta raba jikinta da nata amma hannunsu a tsarke. "My Preety Areefa". Murmushi Areefa tayi kafin ta sake duban agogo bakwai daidai da sauri ta zare hannunta tayiwa Maama sallama ta fice daga cikin dakin. Motarta ta dauka kirar Benz kalar Ash sai kyalli take yi domin tayi alkawarim yau zata baiwa Dr.Erena mamaki zata nuna masa kulawa ta musamman wanda sai ya raina kansa motar shine ya bata ita amma bata taba amfani da ita ba sai yau domin dai ta nuna eh tana son sa din amma da alkawari tayi bazata taba amfani da wani abu daga dukiyar da yake mata kyauta a ciki ba. Da wannan tunanin ta fice daga gidan nasu ta dau hanyar Company din zuciyarta sai faman zillo take yi mata gani take yi abun kamar a MAFARKI ba gaske ba a haka har ta isa Company din tans yin Parking taji ana kokarin buɗe murfin hakan ya daure mata kai da sauri ta dubi glass din ganin wanda yake tsaye ya sanyata ware idanu da mamaki kafun taja guntun tsaki can kasar makoshinta sannan ta buɗe murfin tana kokarin sako kafa waje ya tokare a bakin kofar ya daura hannunsa saman murfin dayan hannun nasa rike da key yana faman kaɗawa sai murmushi yake zabgawa kamar tsohon da ya samu kyauta yar sha bakwai a bagas ko dayake a bangaren Dr.Erena yadda yake jin son Areefa a zuciyarsa gani yake yi ta fi ko wacce mace dake numfashi a doron duniyar nan so yake yi mata mai ansa suna so zai iya sadaukar da komai domin yaga ya mallake ta ko da kuwa zai rasa komai na shi na duniyar nan son Areefa ya rigaya ya gama tafiya da imaninsa sosai ya zautu akan sonta numfashi ya ja idanuwansa na kara lumshewa da wani irin yanayi da yake jin zuciyarsa na kara jefashi a ciki akan Areefa. "Kin makara yau da nayi tunanin ba zaki zo ba har zan bi sahu". Gaban tane ta ji ya yanke ya fadi jin da tayi yace zai bi sahu ita dai a iyakar zamanta dashi bai taba zuwa gidan su kuma bata taba jin yace ya sani ba yayi nacin ta kai shi amma ta kiya wani yawu ta haɗiye mai tauri kafun ta dube shi da murmushin yake a fuskarta. "to da kake cewa zaka bi sahu ina zaka kai da baka san gidan mu ba". Daga kafaɗa yayi yana mai kara juya idanuwansa akanta. "wai shin me kika mai dani ne kin dauka son da zan miki zai zauna a raina haka ba tare da na san gidanku domin zuwa kai ziyara ba to ko jiya naje gidan ku lokacin kina nan wajan aiki ba tare da kin sani ba". Wani irin dokawa taji gabanta yayi da tashin hankali runtse idanu tayi lokaci guda kanta taji yana sarawa shikenan asirinta ya tonu ta gama yawo in har Dr.Erena ya ga Hajiya Layla ta tabbata kashinta ya bushe zuciyarta ta shiga kara mata kwarin gwuiwa akan cewa 'ke kin fiye karaya da yawa ki bari ki ji wani gida yaje mana kuma inda yaje gidanku ai da hajiya Layla ta fada miki tun jiya din'. Wani numfashi taja gami da buɗe idanu tana mai kakalo murmushin dole don bata son ya gane halin da ta fada aiko tana daga idanuwanta ta dube shi wani kallo taga yana yi mata kamar na tuhuma. "Uhmm ban yarda ba ai in da kaje da an fada min". Murmushi yayi yana kara gyara tsayuwarsa kafun ya nuna ta da hannu kamar zai lakace mata hanci. "Bosso Lowcost gida mai lamba 112 gidan Alhaji Saifullahi Suraj". Wata irin ajiyar zuciya tayi lokaci guda jin sunan da ya fadi tabbas ta gane sunan da ya ambata gidan da za su zama iyayenta ne da Alhaji Abdulwahaab ya zo ya sanar da Hajiya Layla ajiya tabbas tayi mamakin amma da ya san gidan cikin nuna mamaki ta dube tana kara fara'arta. "Amma nayi mamakin yarda akayi ka sani fa". "Abu mai sauki ne a gareni kin ga tashi mu shiga daga ciki nan yayi hanya da yawa bana so a zo wuce wa ana kalle min kenan wannan hadaddiyar kwalliyar da kikayi mani domin na tabbata don ni akayi mata kuma zan saye ta da farashi mai tsada ke dai meke mu shiga daga ciki". Mamaki sosai ya kama Areefa ganin yarda yake rawar jiki ba tare da nuna isa da izzar nan tashi ba da yake da ita kamar bashi ba ko da yake kadan daga makircinsa ne zai iya fiye da haka don ganin ya cimma burinsa akan abin da yake so a hankali ta zuro kafafuwanta ta mike bayan ya matsa ta dauko jakarta tana kokarin dauko wayarta taji ya anshe jakar da sauri ta dago ta dube shi ba tare da tace dashi komai ba tana kokarin mai da kofar motar ta rufe nan ma da sauri ya sanya hannu ya rike yana mai sakar mata tattausar murmushi yana girgiza kai matsawa tayi sannan ya rufe kofar kafun yayi mata nuni da hannu su tafi amma ta kiya ta mika masa hannu ya bata jakarta da ya rike kamar wata uwargijiya da bawanta sai da tayi da gaske tana nuna rashin amincewarta sannan ya bata suka jera don cewa yayi bata isa ta taka ita kadai ba ba yarda ta iya haka suka jera din kamar wasu mata da miji shi kuwa sai rawar jiki yake yana faman yashe baki yana zuba surutu. *_Kamala Minna_*😘😘😘😘 [9/16, 10:01 AM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA ARBA'IN DA BIYAR. Duban juna suke yi cikin tsanar da zuciyarsu take mika su akai ji suke yi kamar su shaki juna da kunci da takaicin da suke ji a tsakanin junansu sai faman huci suke yi kamar wasu mayunwatan zakuna. Dr.Karami ya ja wani dogon tsaki kafun ya juya ya dubi kofar gidan su Mariya da wani irin yanayi mai girman gaske yana jin yarda zuciyarsa ke harba da sauri-sauri komai yake ji ya jagule masa gabadaya tunaninsa ya tsaya cak! Kwanyarsa sai kamawa take yi da wuta tana kokarin babbakewa numfashi yake ja yana jin yarda kirjinsa ke wata irin kartawa da tashin hankali mafi girma a filin duniyarsa juyawa yayi da idanuwansa da suka fara kaɗawa ya kalli Dr.Aqeel dake ta faman hura harci kamar zai ci babu. "ka rubuta ka ajje bar ganin abotar da ke tsakanina da kai wallahi sai na shayar da kai ruwan mamaki a filin duniyar nan wallahi kayi kadan ka wulakanta ni a gaban wacce nake so har kake ikirarin ban isa ba to ka jira lokaci zai zo zaka ga yarda zan rabaka da wacce kake cewa kai kafi cancanta da ita". Ya karashe yana nuna Dr.Karami da dan yatsa cikin tsananin bacin rai mara yankewa da sauri ya juya yana kokarin barin wajan amma jin Dr.Karami yayi gyarar murya mai sauti ya sanya shi juyowa murmushi ya gani dauke a fuskarsa mai ma'anoni masu yawa. "karka manta da abotarmu domin ban sako ta a ciki ba amma tun da kace mu ajje komai a gefe to nima zan dauko makaman yaƙi na kuma za a buga ni da kai a ga wanda rana zata rigashi faduwa". Kallon na raina wayon ka Dr.Aqeel yayi masa ya ja kwaɓa. "Ok Hakan na da kyau ina tsumayenka". Yana karasa fadin haka ya juya da sauri ya faɗa cikin motarsa ya fizgeta kamar wanda zai tashi sama. Sosai tashin hankali ya bayya a fuskar Dr.Karami duk juriya da kai zuciya nesa da yake yi akan sabon halin da Dr.Aqeel ya kirkira ya dorawa kansa abin da bai taba zato ko tsammani ba bai taba kawowa kansa Dr.Aqeel zai iya katse ABOTA dake tsakaninsu ba ya sha mamaki sosai akan haka zuciyarsa ta jima tana ciwo akan hakan yayi hakuri ya kau da kai amma sai da ya sanya shi tsayawa ya dube shi har suka fara SA'INSA a tsakanin su. Tun ranar da aka sallamo Mariya daga asibiti gabadaya ya ga ya rikice masa musamman da yaga Mariyar sam taki kula kowa a tsakanin su ko kallon banza ba su ishe ta ba amma shi ya danne zuciyarsa bai nuna komai ba sai shi ne zai dinga ajje masa bakaken maganganu ba tare da laifin sa ba domin shi dai bai ga abin da ya aikata masa ba har da zai din ga daukarsa a wani macuci har yake ikirarin haduwar su ba tayi kyau ba. Jingina yayi da bayan motarsa yana harɗe hannayensa a kirji sosai ya runtse idanuwansa jin yarda zuciyarsa ke kartawa kamar zata yayyage komai yake ji yana zama kunci gareshi komai ya sauya masa sosai yake jin yarda so yake wahalar dashi bai san so haka yake ba bai san ana faɗawa har haka a cikin so ba bai taba tsammanin zai ganshi a DUNIYAR SO yana gararamba ba amma yau shi yake yawo a ciki kamar wani wanda bashi da mafadi ya fado duniyar nan. Numfashi ya kuma ja kafun ya haɗe wani yawu mai tauri ya dubi kofar gidansu Mariya na ba dadi yau cikin satin sa na uku kenan yana zuwa amma Mariya taki kula shi ko fuskarta taki bari ya gani tun ranar da suka dawo da ita gida aike goma zai amma ba biyan bukatar ko daya daga ciki tashin hankalin sa na daduwa abun ya zame masa goma da ashirin ga lamarin Mariya ga wannan shi kuma yana masa hayaniya akai can kuma gida Hajiya ta saka shi gaba bai san me zai yi ba kansa kara kamawa da wuta yake yi ya kasa yin wani tunani ma na kirki ko zai samu mafita. Ya jima tsaye a wajan kafun ya yanke hukuncin barin wajan domin ya tabbata ba fitowa za tayi ba shikuma ba iya shiga gidan zai yi ba domin kuwa gabadaya bai son su hadu da Umma kwata-kwata. Yana kokarin shiga motarsa ya hango Mu'azzam ya fito da gudu yana waige da alamun biyo shi akayi da sauri ya dakata yana mai da kofar ya rufe kamar daga sama ya hangota ta tunkaro kofar fitowa tana ta faman kiran Mu'azzam amma ina sai kara wutar gudun sa yake yi wata irin mutuwar tsaye yayi ganinta ta canza sai yaga ta kara masa kyau da haske sai dai ta kara ramewa sosai harɗe hannayensa yayi a jikinsa kirjinsa da yake faman dokawa da sauri-sauri a daidai lokacin Mu'azzam ya iso gareshi ya kankame shi yana neman ya ceceshi amma shi ina fuskarsa da komai nasa na kan Mariya a daidai lokacin ita kuma ta dube she wata irin razana tayi kafun idanuwanta su yo waje sosai da sauri ta juya ta fada cikin gida cikin wani irin hali mai ciwo a zuciya. Ya shafe lokaci kafun ya ja wani gwauron numfashi mai sauti ya durkusa ya dafa kafadar Mu'azzam yana kallon sa abin mamaki fuskar Mariya yake ganin tana yi masa gizo tana mai sakin tattausar murmushi a gareshi sai da Mu'azzam ya taba masa fuska sannan ya dawo hayyacinsa yana dubansa kafun ya ce dashi. "Me kayi aka biyo ka da gudu haka hala rashin ji kayi ko?". Juyawa yayi ya kalli kofar gidan kafun ya dubi Dr.Karami da ya kureshi da idanu. "Yah Mariya ce ke kuka a daki shine na fadawa Umma kuma ta hanata kukan to shine don Umma ta shiga bandaki shine ta biyo ne don ina ce mata mai kukan banza". Dariya Dr.Karami yayi amma cikin zuciyarsa ji yayi wani zafi na kawo masa farki sosai tashin hankalinsa na daduwa kalmar 'kuka' da yaji Mu'azzam ya ambata tana yi ita Mariyan sake daga kai yayi ya dubi kofar gidan yaji kamar ya mike ya fada cikin gidan ya lallashe ta. "je kace ina kiranta". Ya fadi yana dubansa cikin idanu shima Mu'azzam din dubansa yake kafun ya shiga girgiza kai. "a,a dukana za tayi kuma ko an aika ta zo ba ta fitowa kullum". "Me yasa?". Ya fadi bugun kirjinsa na sauyawa da sauri-sauri Girgiza kai yayi kafun ya sake kallon kofar gidan. "nima ban sani ba kawai dai kullum a daki take zama ba ta fitowa ko Umma bata tayawa aiki". Runtse idanunsa yayi jin wani abu ya tokare masa zuciya kafun ya sake fadin. "Ba ta da lafiya ne". "Tunda ta dawo daga asibiti shikenan ina ganin kila bata ji sauki bane". Mikewa yayi ya saka hannu cikin aljihunsa ya zaro kudi masu auki ya mikawa Mu'azzam girgiza kai yayi alamun ba zai ansa ba sai da yayi dakyar sannan ya ansa. "kace ina gaida Umma da Ita Mariyar kaji yi maza ka koma gida ba wanda zai dakeka". Da gudu kuwa ya juya yayi gida shikuwa jin gina yayi da mota yana faman mai da numfashi sosai yake jin zuciyarsa wani iri jin halin da Mariya take ciki ji yake kamar ya kakkare mata damuwar ya dawo da ita kansa ya sani har da laifinsa wajan sanyata ko wani hali ta fada yana da kamasho in da ya san haka rayuwar zatayi musu inda ya san ALKALAMIN KADDARA haka zai rubuto musu wannan rayuwar da bai yi SAKE wajan bayyana mata yana son ta ba da ya furta mata tun lokacin da yake ganin bata cancanta ba ya san komai daren dadewa zata koyi son shi kuma zata ajje kalmar so da ya fadi mata tun lokacin baya har zuwa lokacin da za ta gane meye SO. Da wannan kuncin zuciyar ya shiga motarsa ya bar kofar gidan kwanyarsa sai wuta take kokarin kamawa da ita gabadaya ya rasa me ke masa dadi a rayuwarsa dole ya san abin yi dole ya fuskarci wannan kalubalin dole ya nemi mafita a gareshi. ******** Tana zaune ta na aikin Cake wanda ya zama yanzu ita ce take yinsa Mariya ta zama abin da ta zama sosai lamarin na Mariya ke sha mata kai ta rasa mai ke damun 'yarta ta yau kusan wata guda kenan tun da aka sallamota daga asibita ta rasa gane kanta kullum cikin kuka take kullum cikin damuwa bata da aikin yi sai kuka abin na taba mata zuciya tayi faɗan tayi rarrashin amma bata sauya zani ba har ta zurawa sarautar Allah ido ta sani suna cikin yanayi na rayuwa duk yarda ta zo musu dole su anshe ta duk wani abun dake faruwa dasu na dadi da rashin sa ALKALAMIN ƘADDARAR su ce a haka ba yarda za suyi... Tunanin ta ya katse lokaci guda da hanzari ta dawo hayyacinta jin an kwaso da gudu anyo waje gabanta ya yanke ya fadi daga idanuwanta tayi cikin fargaba da tsoro duk a tunaninta Mariya ce amma sai taga akasin haka Hafsat ce ta fito da gudu daga dakin Goggo Marka ta zube tana ta faman amai da kakari kamar wacce zata amayar da 'yan hanjin cikin ta amai take yi wanda ba komai a cikinsa sai ruwa da majina sosai ta rike cikinta tana faman nishi tana murkususu kamar wacce akayiwa dukan shan gishiri. Da sauri Umma ta zare hannunta cikin kwabin da take yi ta dauraye hannayenta ta mike kan kafafuwan ta da sauri ta karasa inda Hafsat take wacce ta gama galabaita rikota tayi tana mata sannu gabadaya jikinta ya saki sai faman nishi take yi kamar wacce rai ke kokarin ficewa daga jikinta sosai Umma ta tauyasa mata ganin irin halin da take ciki lokaci guda duk ta zurma kamar wacce take amai da guda. Ruwa ta debo ta bata ta dauraye bakinta sannan ta wanke mata fuska ta taimaka mata ta mike ta raka ta daki ta kwantar kafun ta dubeta ganin ba kowa a dakin. "Dama baki da lafiya ne ina Goggo din take?". Banza tayi da ita jin yarda cikinta da kasar mararta ke kartawa da wani irin azababben ciwo kamar yan hanjinta zasu zazzage sai faman juyi take tana cizon laɓɓanta idanuwanta a runtse sosai zuciyar Umma ta karyewa da yanayin da ta ganta a ciki sai faman sannu take mata jin ta kasa bata ansar tambayar da tayi mata sai da ta jima a tsaye ganin Hafsat ta lafa da murkususun ya sanyata juyawa tana kokarin fita har ta daga labule sai ga Goggo Marka ta sanyo kai ita da sauri ta ja baya Goggo Marka ta shiga dubanta da wani irin yanayi na tuhuma kafun ta leka cikin dakin ta hango Hafsat a kwance sake dubanta tayi. "Lafiya me ya shigo dake dakina". Ta fadi cikin tsawa tsawa da nuna bacin rai "A,a Hafsat naga ta fito tana ta kalaya amai shine na taimaka mata ban san bata da lafiya ba". "Ba ta lafiya fa ? Kika ce injiwa ya fada miki lafiyarta kalau sai dai in wani abu taci yake tayar mata da zuciya har ya kaita ga amai".. Yanayin da take maganar kawai zaka kalla ka gane bata da gaskiya da sauri ta shigo dakin har tana bangaje Umma kayan da suke hannunta gabadaya suka watse Umma tabi kayan da kallo lokaci guda gabanta ya yanke ya fadi ganin kulin maganguna har su mataccen ƙadangare da sauri ta ja da baya ita ma Goggo Marka kayan tabi da kallo kafun ta dubi Umma a dan tsora ce ta shiga tattare kayan tana cewa. "to ki fita mana ko kin tsaya kina kare min kallo ko da kwai wani abu ne?". Tana magana jikin ta na rawa da sauri Umma ta fice daga cikin dakin gabanta na kara tsananta faduwa sai sunayen Allah take kira sosai zuciyarta ta shiga zargin abin da tagani fata take yi Allah yasa hakan kar ya tabbata kar dai ace wani abun Goggo Marka take aikatawa domin sosai ta ji a jikinta akwai wani abu a boye dangane da abin da ta gani a yanzu ta jima tsaye a kofar dakinta tana tunani kafun ta isa wajan aikin da take yi gabadaya taji ya kuma sure mata kwasar kayan tayi ta fada cikin dakinta... *_Kamala Minna_*😘😘😘 [9/17, 8:26 PM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA ARBA'IN DA SHIDA. Zuciyarta zafi take sosai kwanyarta sai kokarin kamawa da wuta take yi ta rasa komai nata mai armashi ta rasa duniyar guntun farin cikinta dake rayuwarta sosai take cikin yanayin kunci zuciyarta sai faman yayyagewa take yi da girman tashin hankalin da take ciki kuka ya daina samun gurbi a idanuwanta HAWAYEN ZUCIYA su ma kan su sun dai samun gurbin zuba komai ya kafe komai ya daina samun numfashi mai kwari daga gareta ba ta san ya zata kwatanta wannan lamarin ba bata san ya zata dauke shi ba bata san mai yasa duniyarta take kokarin yamutsewa ba koma tace ta ya mutse ALKALAMIN KADDARA yayi rubutu mai tsauri akanta bata yi tsammanin rayuwarta zata kare a haka ba farin ciki babu shima kwanciyar hankali babu komai da komai babu kawai dai... Wani irin kartawa zuciyarta tayi da hanzari ta mike daga kwancen da take tana sanya hannayenta duk biyu tana dafewa idanuwanta a runtse kamar wacce ake sokawa karfe mai tsanani jar wuta a jikinsa numfashi take da kyar tana jin kirjinta na kara tsananta bugawa mikewa tayi kan kafafuwanta tana faman cizon laɓɓa kamar zata fizge su daga mazauninsu. Kai kawo ta shiga yi cikin dakin a hankali tana duban su Umma da suke barcinsu cikin kwanciyar hankali ba tare da matsala ba sosai take tausayin kanta sosai take ganin kamar ita kadai ce a filin duniyar nan take cikin tashin hankali gani take kamar ita kadai ne so yake bugawa yadda ransa ke so kamar wata ball bata san ya zata dauki AL'AMARIN SO ba a filin rayuwarta bata san ya zata kwatanta bala'in da fada ba A DALILIN SO ba tana shakka akan cewa so yana da dadi gaskiya ba za ta amince da haka ba so guba ne ba komai ba. Haka tai ta safa da marwa a tsakar dakin har zuwa wani lokaci mai tsayi cikin DUHUN DARE ba tare da ko yaya ne barci ya so kama ta ba in aka ce ma barci zai zo wajan ta zata karya ta domin kuwa ita a karan kanta ta manta yaushe rabonta da yin barci mai ansa suna barci... "Ke Mariya wai lafiyarki kalau kuwa?". Kamar daga sama taji muryar Umma a dan razane ta juya ta dube ta zaune ta hangi Umma ta kafeta da idanu kafun ta cigaba da fadin. "Ke yanzu fisabilillahi kina ganin haka ya dace miki Mariya kina zaton wannan abin da kike yi shi ne zai zame miki mafita a filin duniyarki bana zaton haka wannan damuwar da kike shiga ba karamar matsala zata jefa ki ba ke ko fada ba zakiyi wa kanki ba yaushe ki ka farfaɗo daga ciwo wa yayi zaton ma za ki sake WATA RAYUWA a duniyar nan". Rausayar da kai tashiga yi cikin rashin abin cewa ta sani duk maganganun da Umma take fadi akanta gaskiya ne amma ita bata san ya zata koyi duk wannan abubuwan ba zuciyarta sosai da sosai take zafi sosai take cikin tashin hankali wanda ba ta san ya zata kwatanta shi ba. "Zo ki zauna muyi magana". Cewar Umma cikin Muryar rarrashi da tausayin 'yar tata a hankali Mariya ta ja jiki ta isa kusa da ita ta zauna kafun ta dago ido ta dubi Umma jikinta ya shiga rawa kamar wata mai jin sanyi. "Umma ina cikin bala'i ban san ya zan kwatanta shi ba bana zaton na shigo duniyar nan a nasara bana tunanin akwai wata rayuwa da zan yi har karshen numfashi na bayan wannan...". Sosai tausayin ta ya kara rikita zuciyar Umma nan da nan ƙwalla suka tarun mata a ido bata bari Mariya ta gani ba domin kuwa ita ta san halin da take ciki akan duk matsalolinta amma bata nuna mata ba ta son abin da zai kara dagula mata lissafi dakatar da ita tayi. "ki daina fadin haka Mariya na sha fada miki duk abin da ki ke ganin yana faruwa da baya dama tun fil'azal ALKALAMIN KADDARA ya zana masa haka a KUDINSA don haka Mariya ke daina cewa ke ce kika fi kowa rashin rabo a duniyar nan ke taki matsalar kika sani in da zaki ga na wani zaki sha mamaki zaki ce ke ba komai bane ya same ki godiya zakiyi wa Allah duk wannan abubuwan suna cikin KUDIN JARABAWARKI...". "Sauki fa kika ce Umma?".. Mariya ta fadi da wani irin yanayi mai karya zuciyar mai sauraronta kafun ta ja numfashi tana tura laɓɓanta cikin baki. "bana tunanin haka bana zaton akwai wanda ya kai ni rashin nasara a filin duniyar nan...". Da sauri Umma ta rufe mata baki muryarta na karyewa kamar mai son fashewa da kuka. "A,a Mariya ki daina yawan batun nan zaki iya yin saɓo Allah zai yi fushi dake ki dinga tunanin bayanki ki dinga tuna wanda ya fiki Mariya akwai wanda yafi ki da yawa su zaki duba domin ki tabbatar da cewa ke rayuwarki ma a haka akwai farin ciki shin kina tunani kuwa akan wanda suke faɗowa duniyar ba tare da komai ba ba uwa ba uba ba dangi shin bakya tunanin irin rayuwar da suke yi shin kina tunanin in suka shiga matsala akwai wanda yake rarrashin su ke ki godewa Allah kina da masu duba ki har su ji ƙan ki Mariya rayuwar nan da kike gani ba wai farin ciki bane a cikinta ba wani nishadi a cikinta duk wanda kika ji yace duniyar nan akwai dadi to ki tabbatar auren sa duniyar tayi ki sani duniyar nan ba wai zama ake yi na dindindin ba komai dake faruwa jarabawa ce akwai ranar da komai zai sauya kuma zai canza...". "zuwa yaushe Umma zuwa yaushe kike tunanin rayuwa zata sauya bana tunanin haka bana tunanin rayuwa zata sake buɗe mana wani shafi bacin wannan ki duba tun da na ta so rayuwa take juya mana baya rashin gata rashin Uba rashin kwanciyar hankali komai ma Umma babu a rayuwar mu ta yaya kike zaton zan yi farin ciki?". Maganar take yi cikin rashin hayyaci muryarta na kara buɗewa bakinta sai rawa yake yi Umma kallonta kawai take yi tana faman gyaɗa kai hawaye sai bin kumatunta suke yi bata san ya zata kwatanta wannan al'amarin ba ita gabadaya komai ya kwance mata komai ya kara dagule mata numfashi ta ja mai karfe kafun ta hadiye wani yawu mai tauri ta sake duban Mariya bayan ta dauke hawayen da suke faman zubo mata gabanta yana todakawa so take yi tayi magana amma tana tsoron yarda komai zai watse in batayi wasa ba amma ana ta tunanin ita ce kawai hanyar mafita a garesu. "Mariya mai zai hana ki zabi daya a cikin su tun da abin da ya kasance haka duk wannan kai ruwa ranar da ake yi bana tunanin zaki iya zama matar su su duka mace bata auren namiji sama da daya maza ne suke da wannan damar ta aure mace sama da daya kokari zakiyi ki baiwa zuciyarki juriya da hakuri ki runtse idanu ki zabi daya a cikin su". Galala Mariya tayi da baki tana kallon Umma da wani irin yanayi gabanta na tsananta bugawa kafun wata dariya ta kwace mata kamar wata sabuwar kamu sosai take duban Umma wasu hawaye na zubo mata da take jin su kamar garwashin wuta suna saukar mata a fuska laɓɓanta ta ciza sosai har sai da taji zafi ya ziyarce ta kafun ta sake su. "Zabi kuma Umma? bana tunanin cikin UKU BALA'I zan iya daukarwa kai na daya gaskiya bana tunanin a filin duniyar nan ko zan rasa mai so na zan iya daukar wani a cikin su bana son su su dukan na hakura da su domin kuwa komai ya faru dani a dalilin su ne duk wata bakar rayuwa da wahalar ta da na shiga a dalilin su ne ba su da tausayi ba su da imani sam a zuciyarsu suna son kan su da yawa in da suna jin tausayina wallahi ba za su yi mani haka ba Umma WASU MAZAN san kan su kwai suka sani da burinsu da suke fatan cimmawa akan abinda suke so ba ruwan su da abin da zai faru in dai ba akan su ba ne". "A,a Mariya ki daina fadin haka duk ba mafita bane mafitar kenan ki zabi daya a cikin su dolen su ne su kyale ki tun da ba dukan su zaki hada ki aura ba miji daya a ka sani mace na aura a al'adance haka a addinance". Wani murmushi mai ciwo ta saki. "Bana tunanin zan iya daukar daya daga cikin su...nifa Umma na dawo daga rakiyar su a rayuwa ta ba zan sake kokarin faɗawa matsalar rayuwa A DALILIN ƊA NAMIJI ba an yi na farko ba za a sake yin na biyu ba na gwanmace in zauna haka ba aure har na karashe rayuwa ta...". "Ya isa haka Mariya nace miki ya isa haka abin naki yana neman zama rashin hankali kuma kina nuna nufin don wannan abin ya faru dake shikenan kuma kin yanke rahama a rayuwarki kenan butulci zaki yi wa Allah to tun wuri ki san abin yi domin ba zan lamunci wannan shirman naki ba". Tana gama fadin haka ta koma ta kwanta hakan ba karamin tashin hankali ya saka Mariya ba duban Umma take yi da mamaki zuciyarta sai faman bugawa take yi sosai take jin wani iri maganganun Umma sai tsananta sauti suke yi a cikin kanta runtse idanu tayi tana daura hannayenta saman kirji tana jin yarda yake bugawa cikin wani irin yanayi sake buɗe idanu tayi ta kalli Umma wacce tayi shiru ta san ba barci take yi ba sosai ta lura ranta ya dan sosu kin amincewa da tayi da maganar ta gyaɗa kai tayi kafun ta zabga tagumi hannun bibbiyu. ****** Tunda Baseera ta shigo take kallonta da wani irin yanayi na tausayawa ganin yarda Mariya ta fige ta kanjame kamar wata mai amai da gudawa ko da yake irin wannan bala'in da take ciki komai ma zata iya zama numfashi ta ja tana zama bakin katifar da Mariya take zaune tayi mata kuri da idanu sai faman yake take yi wanda sam bai mata kyau ba. "Kin gama fushin da ni kenan kin ga dama kin zo". Cewar Mariya tana hararar Baseera da jikinta ya gama yin sanyi da Al'amarin Mariya sai faman gyaɗa kai take yi zuciyarta na tsananta bugu kafun tayi kokarin kirkiro yaƙe ita ma ta yi mata. "Ban san me yasa har yanzu Baseera ki ka kasa daidai ta komai ba dama fa a hannun ki take amma kin kasa amfani da ita duk wannan abun dake faruwa ke ce kike da mafita amma kin ki amfani da ita ban san me yasa ba?". Ta karashe tana janyo hannun Mariya ta damke a nata nan da nan sai ga hawaye a idanuwansu su duka numfashi suke saki a hankali Mariya sosai take jin wani iri a zuciyarta ana cewa tana da mafita a hannu amma ita ta ka sa gane a ina mafitar take a gareta komai ta kasa tunani akan sa kwanyarta a tsaye take cak! tana babbakewa bata da wani kuzari ko jarumtar yin wani tunani. "ki yi kokari don Allah ki samarwa kanki farin ciki da kwanciyar hankali har da muma mu sa mu don Allah". Baki ta shiga motsawa tana kokarin yin magana amma ta kasa sai da ta runtse idanu kafin ta buɗe su da ƙyar ta daga laɓɓanta. "Ban san me zan yi ba Mariya sosai na kasa yin komai bana so wani abu ya sake hadani da su Umma tace wai zabi na gareni har da mafita kamar yarda ke ma kika ce amma na kasa tuna haka bana tunanin haka zai yuwu". "Mariya ke ki da wannan damar sai dai kin kasa amfani da ita ya kama ta ace kin fidda daya daga cikin su ina tunanin haka shi ne kawai mafita a garek...". Da sauri ta fizge hannunta tana ja da baya kamar wacce aka doɗanawa garwashin wuta duban Baseera take yi cikin wani irin yanayi idanuwanta sun kara kaɗawa sun yi jajir sai faman hirji take yi tana jan numfashi yana kokarin kwace mata kai ta ke girgizawa a hankali tana mai runtse idanunta kafun ta kai hannunta daidai kirjinta ta dafe da karfin tsiya. "Ba zan iya ba Baseera bana son su na tsane su". "Zaki iya Mariya za ki iya ki na son su baki tsane su ba ni na san haka daurewa zaki yi don Allah". Bude idanunta tayi da sauri tana duban Baseera kafun lokaci guda ta kifa kanta kan katifar tana faman nishi dakyar kamar wacce aka shake a makoshi.... *_KAMALA MINNA_*😘😘😘😘 [9/17, 8:28 PM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA ARBA'IN DA BAKWAI. Abu kamar wasa Mariya zuciyarta da kwanyarta sai kuwwa suke mata mai sauti akan batutuwan Umma da Baseera sosai take jin lamarin ya fara samun karbuwa a gareta zuciyarta na ta kokarin bata dama tayi abin da suke bukata amma ta rasa ta yarda zata fara domin kuwa wani bangare na zuciyarta sai safa da marwa yake yi wajan yanke hukunci kan lamarin. Numfashi ta ja kafun tayi shiru tana mai tallaɓe haɓarta kamar daga sama ta jiyo kuwwa daga waje da ihu shiru tayi tana sauraron kafun daga bisa ni tayi hanyar fita tsakar gidan Umma ta hango tsaye tana kallon ikon Allah Goggo Marka ce ta turmushe Hafsat sai faman jibga take yi kamar ta samu jaka daga ita sai dan fatari a kugu zanin ya fadi Mariya da take kallon ikon Allah bata san lokacin da dariya ta kusan kufce mata ba duban Umma tayi cikin yanayi na mamaki abin da tunda take a rayuwarta bata taba gani ba shine yau yake faruwa tabbas in da sauran numfashin ka a duniya kana DA SAURAN KALLO. "Umma me ke faruwa ne hak...?". Da sauri Umma ta daga mata hannu ba tare da tayi mata magana ba idanuwanta na kan Goggo Marka da ta zage sai jibgar Hafsat take yi kamar Allah ya aikota sai faman numfashi take ita kuwa Hafsat sai zunduma ihu take yi tana kokarin kwace kanta. "Umma zata kashe fa bai kama ta ki bar ta tai ta dukan ta b...". Sake daga mata hannu tayi a karo na biyu ta juyo ta dube ta fuskar ta da yanayin bacin rai sosai da sosai kafun ta hadiye wani yawu mai tauri mai nuna a wuya take. "Yo meye na ki a ciki ta kashe ta mana wa tayi wa jikarta ce komai tayi mata wallahi ko a jikina". Nan da nan Mariya tayi rau-rau da idanu tana duban Umma jin abin da tace. "Haba mana Umma mai yasa zaki ce haka? kina kallo fa irin dukan da take yi mata bai kamata ba...". "A wajan ki ne kike ganin bai kamata ba Mariya..tun dazu nake jin haniyar su ina zaune a nan daga cikin dakin su ban tanka ba sai da naji Goggo na zunduma mata zagi kamar wata wacce ta kirkiri maguzanci shine fa na tashi domin bata hakuri in laifi Hafsat tayi mata amma sai ta hada dani tana tsine min har da iyayena take anbata har tana cewa in har ni ba shegiya bace na fice na ba su waje". Umma ta karashe tana dauke hawayen fuskarta da suke ta faman zuba kafun ta sake nisawa cike da bacin rai. "ko ni shegiya ce wallahi dole in bar su in dai ina da zuciya balle kuma uwa da uba akwai su ban hanaki ba zaki iya zuwa ki cece ta domin 'yar uwarki ce ta jini amma ni kam wallahi a,a haram shan giya gidan liman". Ta karashe tana karasawa wajan da take wankin kayanta ta cigaba da yi sai faman ajiyar zuciya take da wani irin yanayi na takaici zagin da Goggo tayi mata tun da take a rayuwarta ko kwatankwacinsa ba a taba yi mata ba. Jikin Mariya yayi sanyi sosai tausayin Hafsat take sannan kuma maganganun da Umma ta faɗa mata suna ci mata zuciya sosai taji ranta ya baci tun da taga Umma na hawaye ta tabbata yau an kaita bango numfashi ta ja mai tattare da bacin rai kafun ta dubi Umma wacce take faman dirza kayan wankin kallo daya zakayi mata ka gane sauke haushinta take a jikin kayan da saurin Mariya ta isa gareta ta riko hannunta dago idanuwanta tayi wanda sukayi face-face da hawaye sun kaɗa sun yi jajir sosai hannu ta saka ta na goge mata su. "Haba Umma me yasa kike zubda hawayenki akan Goggo ya kamata ki saba ba yau bane ta saba yi miki haka...". "Na san ba yau bane amma abin da tayi mani yau na tabbata zai ji ma a zuciyata bai gogu ba duk abin da take yi mani ina hakuri amma yau HAKURINA ya kare ta kai ni bango amma ba komai Allah na nan ai zai yi mani sakayya". Ta karashe tana rike hannun Mariya da take goge mata hawaye da su juyawa sukayi su duka suna kallon Goggo Marka wacce ta dago a wannan lokacin tana faman sakin numfashi kamar wacce tayi gudun faffalaki. "Ni zaki tozarta ni zaki ciwa mutunci ni zaki kwancewa zani a kasuwa to wallahi ba ki isa ba kin yi kadan a yau din nan sai kin koma wajan uwarki ba za ki ja min abin kunya ba a gidan nan haka kawai ina zaman zama na zaki dauko mani ALAƘAƘAI ba garai babu dalili ban san hawa ba kawai sai naji sauka ai da sake wallahi ba a gidan nan ba". Abin da Goggo Marka ta shiga fadi kenan tana faman haki kamar wacce Numfashinta ke gardama sai faman nuna Hafsat take yi wacce ke kwance idanuwanta sun kada sunyi jajir sai zubda ruwan hawaye suke yi tana faman nishi domin ta daku iya dakuwa Duka ta sake kai mata cikin rashin tsammani ta doke mata baki lokaci guda ya fara zubda jini kafun ta shureta da kafa ta wuce bayan ta tsintsine mata tayi hanyar dakinta sai faman zage-zage take yi. Su dai su Umma kasake sukayi gabadaya ta rikita su sun rasa mai Hafsat tayi mata har haka ta duke ta duka mai ansa sun duka haka ko barawo akayi wa wannan dukan sai ya san ya daku a hankali Mariya ta kalli Umma tana faman gyada kai kallon ta Umma tayi ta kau da kai don ta san abin da take nufi a hankali Mariya ta ja jiki zuwa in da Hafsat take bakinta sai zubda jini yake yi idanuwanta na zubda hawaye kallonta tayi kafun ta kau da kai jin zuciyar na tunano mata da kiyayyar da Hafsat ke mata tana jin wani iri da bacin rai amma haka ta daure kawai ta dago ta tana mai zare mata dankwalin kanta tana goge mata fuska da jinin dake zuba a jikinta. "Sannu ko Hafsat me kika yi wa Goggo haka har take dukan ki abin da bai taba faruwa ba?". Ta tambaye ta tana mikar da ita kan kafafuwanta ita kuma sai faman cizon laɓɓa take yi saboda tsananin ciwo da jikinta ya kama yi lokaci guda. "Uban ki tayi min hegiya tsohuwar munafuka in baki sake ta kin bar wajan nan ba in na zo wallahi sai na hada dake". Kamar daga sama suka tsinkayo muryar Goggo Marka na fadin haka da sauri Mariya ta ja baya tana mazurai. "Shaggu na kurya masu gansa kuka a idanu ina ruwan ki da ita kinibabba me ya shafe ki da abin da tayi min in ban da kuturun kinibibi irin na ruwarki shine zaki zo kina tambayar ta". Da hanzari ta ja jiki ta bar wajan tana kallon yarda Goggo Marka ke faman watsa mata banzan kallo kafun ta juya wajan Hafsat dake tsaye kikam. "ke kuma zo ki shige tun kafun nazo wajan nan na karya miki shaggun kafafuwan nan naki bakar munafuka kawai". Kikam tayi ko motsi ba tayi ba sai faman zunburo baki take yi gaba wanda ya fara tasawa. "dake fa nake ko ki zo ki shige ko kuma ki fice daga cikin gidan nan". A hankali ta fara dingisa kafar da tayi mata tsami sosai ta tunkari dakin tana zuwa Goggo Marka ta dungure mata kai tare da hankaɗa ta cikin daki kafun ta juyo ta dubi su Umma tana jan katon zaki. "Tsofaffin munafukai kawai ta Allah ba taku ba". Murmushin takaici Umma ta saki kafun ta ja hannun Mariya su shiga cikin dakin su rai a matukar bace. ***** Tafe take kanta a kasa kamar wata maras gaskiya Hijab din ma sakko dashi tayi zuwa fuskarta yarda ba kowa yake gane waye ba hannunta rike da ledar kayan cefanar Cake a hankali take tafiya kamar wacce bata son taba kasa. Kamar daga sama taji yo Horn din mota da sauri ta dago kai kafun ta shiga ja da baya duk a tunanin ta kan hanya take ake mata horn amma sai ta ga akasin haka motar a tsaye take gefe guda amma sai danna horn ake yi haka da ta gani ya sanyata tunanin ba da ita ake ba da saurin ta shiga waige-waige don ganin da wanda ake amma ba kowa a hanyar sai tsirarun mutane kuma kowa harkar gabansa yake yi koman da kanta kasa tayi ta cigaba da tafiya amma gabanta sai dokawa yake yi domin tunaninta ya bata da ita ake yi hakan ya sanyata kara saurin tafiyar da take yi daidai kwanar da zata shigar da ita kofar gidan su ta ga Motar ta shawo gabanta da gudu cikin tsananin firgici tayi gefe tare da sakin kara mai sautin kayan hannunta duk suka zube kasa don duk a tunanin ta markaɗe ta motar za tayi amma sai taga akasin haka buɗe idanuwanta tayi da suke runtse ta sauke akan motar ganin ana kokarin buɗewa gabanta ne ya yanke ya fadi ganin waye a cikin motar yake kokarin fitowa haɗe fuska ta kare yi ta durkasa kasa tana hada kayanta gabanta sai dokawa yake yi da wani irin yanayi gabadaya jikinta bari yake yi lokaci guda idanuwanta suka kada sukayi jajir duk ta rikice kayan nata ta kasa hada su hannunta karkarwa yake yi kawai. Daddaɗar kamshin turare ne ya daki hancinta lokaci guda ta ja numfashi mai tsayi gami da runtse idanuwa sosai taji a jikinta kallonta yake yi a hankali taji ana ansar ledar dake hannunta cikin rashin kuzari ta saki ledar ba tare da wata gardama ba a hankali ya shiga tattare kayan ya ajje su gefe idanuwansa gabadaya ya sauke akanta yana kare mata kallo kafun lokaci guda ya ja numfashi mai tsayi zuciyarsa na mika shi wani mataki na daban mai cike da abubuwa muhimmai akan Mariya. Mika hannu yayi kamar zai kamo nata hannun da sauri ta mike tana ja da baya idanuwanta cikin nashi suka sarke gabanta ya cigaba da bugawa a wani mataki wanda yake rikita mata tunanin gabadaya ta rikice sai faman rawar jiki take yi zuciyarta taji tana mikata wani sashi na daban mai kokarin canza mata duk wani tunaninta memorinta taji yana kokarin goge haddar da tayi runtse idanu tayi jin wani abu mai kama da kibiya mai tsanin haske ya kufto daga fuskar Dr.Karami mai tattare da lallausar murmushi ta tunkarota kafun lokaci guda ta buɗe idanun nata haske ya mamaye fuskarta wani numfashi ta ja mai karfi kamar zata shiɗe. "Ban san me zan ce miki ba Mariya amma ki sani zuciyata tana matakin da take kokarin tarwatsewa da son ki na azabtu na wahalu lokaci mai tsayi wanda nayi tsammanin rayuwata ta kare ke nan duk a kan ki son ki Mariya sosai zuciyata ta kasa sarrafa kanta a dalilin sonki komai...komai nawa ya canza sosai da sosai duk dalilinki ki dube ni Mariya ni mai son ki ne so na hakika ki daure don Allah karki baiwa zuciyata kunya". Wani irin dokawa zuciyarta tayi wanda har sautin ita kanta sai da ta ji ya bayyana idanuwanta a rufe jin ta take yi zuciyarta na mikata wani mataki da bata tajin taje ba sosai taji kamar kan gajimare take yawo maganganun Dr.Karami suka shiga sauti a cikin kwanyarta mai kara zuciyarta da ruhinta taji suna buɗewa da wani irin yanayi suna ansar sakon Dr.Ƙarami gabadaya taji komai nata kamar sabo komai ya goge sabbin abubuwa taji suna shigarta ta ko ina sake damke idanuwanta tayi kafun ta bude su ta sauke akan sa wani irin kwarjini da haifa take hangowa saman fuskarsa suna kara narkar mata da zuciya cikin wani mataki wanda ba zata iya sarrafa kanta ba. Durkusawa tayi ta kamo hannayen ledan kayanta ta mike sosai kan kafafuwanta da taji suna lauyewa suna kokarin zubda ita kasa kokarin motsawa tayi tana ɗaga kafar guda daya da taji tayi mata nauyi sosai runtse idanu ta sake yi kafun ta tura laɓɓanta duka cikin baki a hankali ta shiga takawa idanuwanta na kara lumshewa gabadaya garin taga yana juya mata ji take yi kamar ba ita ba gani take yi kamar wata MARIYA ce ba ita ba tana ji yana kiran sunanta muryarsa na dakar mata zuciya da kwanya suna kara rikitata amma ta kasa katabus tafiya kawai take yi bugun zuciyarta na kara tsananta sosai a cikin wannan yanayin taji ta cikin soron gidan su lokacin guda ta karasa shiga ta zube tana mai jan wani numfashi mai tsayi dumin hawayen da suka zubo mata ya sanyata buɗe idanu a razane duk a tunanin ta ya biyo ta amma sai ta ga akasin haka bata goge hawayen ba illa wani kuka ta taji ya zo mata tun daga zuciya da ruhi da gangar jiki kukan take yi mara sauti sai faman shassheka take yi kamar wacce numfashin ta zai dauke... *_KAMALA MINNA_*😘😘😘 [9/22, 9:13 AM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA ARBA'IN DA TAKWAS. Cikin kwana biyun da tayi bayan haduwarta da Dr.Karami gabadaya ta gama rikiciwa ta rasa mai ke yi mata dadi a rayuwarta zuciyarta sai faman zillo take akan lamarin sa ta rasa ma me za tayi. A hankali take kokarin saita kanta da samo mafitan da take ganin ya dace da ita sosai take hana idanuwanta barci tana kai kukan ta wajan Allah domin ya zaba mata abin da yafi zama alheri a rayuwarta baki daya. Sosai zuciyarta ke matsewa sosai take jin nauyin da zuciyarta ke yi yana raguwa a hankali sosai take jin ya kamata ace izuwa wannan lokaci ta sarara wa kanta da rayuwarta sosai take jin lokaci yayi da ya kamata ta kawo karshen komai. Amma ta yaya hakan zai kasance ta yaya hakan zai yuwu ba ta san ya za tayi ba sosai zuciyarta ta karkata zuwa ga Dr.Karami yawancin barci in tana yin sa duk shi take hangowa amma bata jin za ta iya aurensa. Amma kuma bata san dalili ba in maganar aure tafi karkata ga Dr.Aqeel tana son Dr.Karami shima Dr.Aqeel tana jin son sa sosai a ranta ba kadan ba sai dai fili mai yawa Dr.Karami ya mamaye mata. Haka rayuwarta tayi ta tafiya har tsayin wata daya amma har lokacin bata yanke hukunci ba ta rasa wanda zata tunkaro ta fada masa halin da take ciki domin samun mafita tana tsoron sanar da Umma domin yanzu duk ta ja baya ta bata dama ita akaran kanta tayi abin da ya dace Baseera kuma har zuwa wannan lokaci taki yarda su hadu domin bata son ta zo mata da wani lamarin na daban bata so ta zaba mata abin da ba shi zuciyarta take so ba Haka dai ta cigaba da dakon wannan lamarin har da karshe ta yanke zuwa gidan su Baseera domin ita kadai ce k'awa shakikiya da take ganin ya dace ta san matsalar kuma ta bata shawarar da take ganin ya dace. Sanye take cikin daguwar riga mai kalar baki da ratsin ja kadan ta sanya jan gyale tayi rolling din shi a kanta sosai ya fito mata da kyanta duk da ba wata kwalliya ba ce ta a zo agani tayi amma tayi matukar kyau takalmi flat ta saka a kafarta sannan ta fito tsakar gida ta tadda Umma zaune ita da Mu'azzam duban su tayi su duka kafun tayi murmushi wanda iyakarsa fuska tausayin kanta da na Umma hadi da na kaninta kawai take ji tunowa da tayi da mahaifinta ko yana ina a halin yanzu Allah masani. Numfashi ta ja mai tsayi har sai da Umma ta jiyo sautin sa juyowa tayi ta dube ta sosai. "Lafiyarki kalau kike wannan doguwar ajiyar zuciyar?". Ta fadi tana kara duban jikinta. Gyaɗa kai tayi tana sake kokarin kakalo murmushi duk da kwallar da ke kawo mata farmaki a idanu. "Ba komai kawai dai...Uhmm yawwa Umma zani gidan su Baseera". Kallon tuhuma Umma ta shiga yi mata na dan lokaci kafun ta gyaɗa kai. "Allah ya kiyaye hanya ki gaida mutan gidan amma karki dade fa kin ga yamma ta fara yi". Ansawa tayi da 'to' sannan ta dubi Mu'azzam da yayi kuri yana dubanta dakune masa fuska tayi cikin tsokana. "Yah Mariya zan biki". Ya fadi cikin sanyin murya zaro idanu tayi waje. "Ni zaka bi caɓ! gaskiya a,a ba zan iya jigilar zuwa da kai ba ban son kaje gidan mutane kana yi musu rashin ji ka bar ni da jin kunya". Ta fadi tana mai kama hanyar ficewa rau-rau yayi da idanu kamar zai yi kuka amma Umma ta hana shi ta shiga rarrashin sa. Hafsat ce ta fito daga cikin daki fuskarta dauke da rashin walwala sai faman ya tsine fuska take yi kallo daya zakayi mata ka gane ramar da tayi ta ɗashe tayi fari sosai ga idanu duk sun zurma tayi firgai-firgai da ita. Mariya dake koƙari ficewa ganin Hafsat ta fito ya sanyata tsayawa tana dubanta kafun ta dubi Umma cikin yanayi na tausayawa a hankali ta shiga motsa laɓɓanta. "Uhmm Hafsa ya jikin naki...". Wata harara da ta maka mata shi ya sanyata saurin tsuke bakinta tana kau da kai zuciyarta take ji tana wani iri tuni ta fahimta har zuwa wannan lokacin ba abin da ya canza a Hafsat duk rashin lafiyar da take fama da ita kamar zata mutu amma bai sanya komai ya canza ba duban Umma tayi itama Umma ita take kallo mai cike da 'Allah ya kara' ta maka mata harara da sauri ta ja jiki zuciyarta na kunci. "Munafukar banza sau nawa zance miki ki daina shiga lamarina ina ruwanki da rashin lafiya ta". Furucin Hafsat kenan ta fadi da kyar kamar wacce akayi wa dole Mariya bata bi ta kanta ba illa karasa fita daga gidan cikin sauri da tayi. ***** A hankali take tafiya zuciyarta ta mika ta can wani waje na daban kawai tafiya take ba tare da ta kula da inda take jefa kafa ba cikin wannan yanayin har ta isa bakin titi ta tsayar da mai Napep tana kokarin shiga wata bakar mota kirar 406 ta zo gilmawa ta gabanta kamar ance ta dago kai ta dubi motar wani irin faduwar gaba taji ya ziyarce ta da sauri ta runtse ido ta bude lokaci guda. Shi din ne ba wani ba har ta mance yaushe rabon da ta ganni a idanuwanta tun lokacin da suka kusan kashe ta sai kuma ranar da ya zo wajan Hafsat abin yayi matukar bata mamaki yarda Huzaif ya kasance mai FUSKA BIYU a gareta yana bibiyarta yana ikirarin yana sonta sannan kuma yana son 'yar uwarta sosai taji lokaci guda ya fice mata a rai wani haushi da takaicin sa ya tsirga mata a rai domin ganin rainin wayo yake musu a tsakaninsu ya mai da su kamar wasu ball ya buga wannan ya buga wannan. 'Mtss. Ta ja dogon tsaki dago kai tayi ta dubi mai Napep wanda shima ita yake kallo haushi ya sake turnuke ta ganin irin kallon da yake yi mata kamar ya ga wata bakuwar halitta. "Tafi abin ka na fasa". Ta fadi cikin haushi da takaici a rayuwarta ta ki jinin kallo shi kuwa kamar wani maye gabadaya ya juyo yana dubanta a hankali ta fara takawa tana barin wajan tana ji yana kiranta amma ko ta kansa ba ta sake bi ba. Da sauri ta tari wani Napep din ta dane tana hango waccan sai faman dubanta yake yi har suka zo suka giftashi suna hada idanu ta galla masa harara gami da jan tsaki. Tafiya sukayi sosai daidai wajan wani Mall ta hango motar Huzaif anyi Parking dinta daga dan gefe ta hango shi shida wata mace ya rike mata hannu sun tunkari cikin wajan zaro idanu waje tayi zuciyarta na harbawa da sauri-sauri kamar zata fallo daga cikin zuciyarta rintse idanu tayi zuciyarta na matsewa da wani irin bakin ciki tana tattama akan Huzaif anya kuwa son da yace yana yi mata na gaskiya ne an ya son gaske yake yi mata? Girgiza kai ta shiga yi da sauri-sauri zuciyarta na mikata can baya lokacin da suka fara haduwa da yanayin da ya nuna mata ta tabbataa akwai alamar tambaya akansa bata san abin da ya shigar mata kai ba har ta yarda dashi bata san me yasa har ta saki da Huzaif ba sosai take ganin wautarta sai yanzu ta hango kuskuren da tayi har ta bashi fili a zuciyarta yake abin da ya ga dama aciki. bata san sun wuce wajan ba sai da suka kai daidai wata hawa taji anyi sama da ita sannan tayi firgigin ta dawo hayyacinta ta shiga ware idanu gani tayi har sun shigo layin su Baseera wata irin ajiyar zuciya tayi mai karfi kafun ta runtse idanunta da wani irin yanayi a zuciyarta ta sanar da mai Napep daidai in da zai sauke ta. Tana sauka ta bashi kudin sa ta dauki hanya domin karasawa gidan a bakin Get ta tsaya ta kwankwasa mai gadi ne ya leko ganin wacece ya saki murmushi ita ma murmushi tayi masa tana gaishe shi ya buɗe mata ta shiga a hankali take tafiya tana tunkarar kofar da zata shigar da ita cikin babbar falon haka kawai taji zuciyarta na kunci tana kuma bugawa cikin sauri-sauri a haka har ta isa bakin kofar ta rike Handle din haka kawai ta ji wata kasala da gajiya ta saukar mata sakin Handle din tayi ta dan ja baya tana ajjiyar numfashi tana mai lumshe idanu kamar mai jin barci a hankali ta sake kamawa idanuwarta a rufe ta tura gami da yin sallama muryar Mami da taji ta ansata ya sanya shiga ciki. Zaune suke ita da Tareeq ya mike sosai kan kujera waya a hannunsa sai faman latsata yake yi Mami da ta ganta ta saki Murmushi kamar ko yaushi da sauri ta isa gareta ta durkusa ta na gaishe ta ansawa tayi kafun ta dube ta sosai. "Ya jikin naki Mariya da fatan dai komai Normal ba abin da ke damun ki kuma?". Gyaɗa kai tayi ganin Tareeq ya juyo da sauri yana dubanta suna hada idanu tayi kasa da kai shi kuwa har zuwa lokacin idanuwansa na kanta ajikinta take jin haka ana kallonta wani tunani ne ya fado mata kar Mami tace bata kyauta mata ba dago kai tayi a hankali ta dube shi. "Ina yini Yah Tareeq". Ta furta murya can kasar makoshi tana rawa bai ansa ta ba illah duban sosai da ya sake yi mata jin da yayi ance bata da lafiya kafun ya numfasa ya ansata ba yabo ba fallasa tare da yi mata ya jiki. Haka kawai taji wani iri yanayin da ya ansa mata cikin izza da nuna rashin baiwa gaisuwar tata muhimmanci ji tayi zuciyarta wani iri duban Umma tayi tana faman yake. "Umma Baseera na ciki kuwa?". "Eh tana ciki yanzun nan ta tashi daga nan wai barci zata yi". Murmushi Mariya tayi tana mikewa kan kafafuwanta duk sai taji wani iri ganin yarda yake kallonta gabadaya taji kafafuwanta suna harɗewa kamar zata zube a kasa sauri ta kara don kar tayi abin kunya agaban wanda bai san ya kula mutane ba in an kula shi mtss ta ja tsaki ta dane sama abin ta har ta kai matakin sauka sannan ta juyawa da kanta kasa aiko sai idanuwansu suka sarke zaro idanu tayi sosai ganin har zuwa wannan lokacin yana kallon ta wani murmushi taga yayi na gefe kumatu tare da lumshe idanu da sauri ta kau da kai tana jin zuciyarta na bugawa cikin hanzari ta bar wajan. Tana isa kofar dakin Baseera ta tsaya cak! tana mai da numfashi me Tareeq yake nufi da ita mai yasa yake yi mata haka me hakan ke nufi wannan kallon na meye yake yi mata ta lura dashi in dai ta zo gidan nan ta same shi gaban Umma ya dinga sha mata kamshi kenan amma in bata nan sai ya dinga jifanta da wani kallo dake faɗar mata da gaba ta rasa me yasa haka. 'me ya shafe ki dashi' zuciyarta ta fadi mata da sauri ta daga kafunta alamun 'babu' ta tura dakin ta shiga ruf! ciki ta same ta waya a hannunta sai faman danne-danne take a waya da sauri ta karasa ba tare da Baseerar ta sani ba ta zaune gefenta tare da sanya dan yatsar ta daya ta ta sosa mata tsakiyar tafin kafarta wata irin razana da ihu Baseera tayi tana mai komawa can gefe ta cillar da wayar saman gado idanuwa a warwaje jikinta sai k'yarma yake yi Mariya ta kwashe da dariya kafun ta ce. "Ke banza ni ce fa matsoraciya kawai". Wata uwar harara Baseera ta cilla mata kafun ta ja wani numfashi mai nuna alamun ta firgita sosai. "Allah ya isa wallahi ke kam an yi muguwa ai wannan sai kiyi ajalin mutum da tsoratarwa wallahi". Ta fadi tana mai sankowa daga gadon tana isowa gareta ta zauna kallon sosai tayi mata kafun tayi murmushi. "Baby din nan fa kyau kike karawa wallahi kamar wata sabuwar amarya meye sirrin ne ko dai...". Sai kuma tayi shiru tana kyalkyalar dariya dubanta Mariya tayi cikin muryar mai rauni. "Magana na zo muyi don Allah Baseera ki bani shawara". Sosai Baseera ta shiga dubanta ganin yarda fuskarta ta nuna alamun damuwa gyaɗa kai ta shiga yi tana kokarin yin magana suka ji an turo kofa gabadayan su suka juya suka Fuskanci kofar Mariya ce ta zaro idanu kafun ta kau da kanta gefe. "Yah Tareeq". Cewar Baseera tana duban sa murmushi ya saki yana duban Mariya kafun ya dubi Baseera ya kashe mata ido daya dakune fuska tayi tana mai girgiza kai ba tare da ta bari Mariya ta ganta ba. *_Kamala Minna_*😘😘😘 [9/23, 9:03 AM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA ARBA'IN DA TARA. Sosai taji a jikinta kamar akwai abin da ke faruwa don haka ta dubi Baseera da taji ita ma tayi shiru tunda ta kira sunan Yah Tareeq dubanta tashiga yi ganin abin da take yi da idanu tana dakune fuska kamar wacce aka tursasa sai tayi abu ba tare da ta so ba. Haka kawai taji gabanta yana faɗuwa dago kanta tayi gabadaya ta sauke wajan Tareeq wanda yake ta faman biyawa Baseera karatu ta hanyar idanu da hannu ganin Mariya ta dago kai da sauri ya wayance yana faman cin magani. "wai shin me ya faru ne naji ihun ki?". Ya fadi yana duban Baseera da tayi tsiru-tsiru gabanta na dokawa tsoronta daya kar Mariya ta gano abin da suke yi a tsakanin su akan ta ne susa keya tashiga yi kamar maras gaskiya tana faman yak'e. "Bakomai Yah Tareeq". Ta fadi tana mai duban Mariya wacce ta komar da kanta kasa tana nazarin yanayinsu tabbas akwai wani abu a boye a tsakaninsu wanda zuciyarta ta tabbatar mata akan ta suke komai haka kawai ta sha jinin jikinta. "Uhmm Yah Tareeq..". Da sauri ya juya har yana kokarin tuntube wajan fita nuni da Baseera tayi masa kamar Mariya ta gano su shi kuma abin da bai kauna kenan sam! Mariya ta gano halin da yake ciki a kanta. Son ta yake yi amma ya rasa yarda zai yi ya fuskance ta ba yarda bai yi da Baseera tayi masa kamfe ba amma ta kekeshe kasa ta ki yarda ba abin da bata fada masa ba akan halin da Mariya take ciki amma ya ki amincewa giyar soyayya sai kwasar sa take yi amma ya kasa zuwa ya tunkari Mariyar. Wani murmushi Baseera ta saki lokacin da ta hango Tareeq na kokarin bugar bango da sauri ta kalle shi shima kallon ta yayi yana dakune fuskarsa sannan ya fice daga cikin dakin.. "Mariya wai shin me ke faru ne naga duk jikin ki yayi sanyi haka". Baseera ta katse shirun da yayi wa dakin ado. A hankali Mariya ta dago da kanta ta dubi Baseera cikin yanayi na tuhuma sai da ta sha jinin jikin ta ganin irin kallon da Mariya take yi mata. Murmushi Mariya ta saki na yak'e kafun ta nutsu fuskarta na komawa yarda take a shigowarta alamun damuwa. "Sosai na kasa fahimtar komai, ban san ya zan fuskanci wannan lamarin ba". Ta fadi tana mai tura laɓɓanta cikin bakinta fuskarta na kara bayyanar da tsantsanr damuwar da take ciki zuciyarta take ji tana kara matsewa da wani irin yanayi mai girman gaske haka kawai taji tana shakka akan ta fadiwa Baseera halin da take ciki a wannan lokacin. Numfashi taja mai tsayi kafun ta mike tsaye tana kai kawo cikin dakin na dan lokaci sannan ta tsaya cak! Ta juyo ta dubi Baseera da tayi shiru tana sauraron zuciyarta itama na ta fadan tsalle-tsalle da fargaban abin da take son kawowa Mariya din so take yi kawai fatanta ya tabbata Allah yasa maganar da Mariyar zata yi ya zo daidai da gaɓar da take so zata yi amfani da wannan damar domin samun abin da take bukata duk da zuciyarta na ta faman gargaɗinta ita akaran kanta jin wani iri take yi kan lamarin amma bata san ya za tayi ba. Mikewa tayi ita ma Baseera tana takawa zuwa inda Mariya take tsaye jikinta na kara karyewa sosai zuciyarta na bugawa cikin wani mataki na rashin tsammani. Dafa kafadar ta tayi tana mai ajiyar zuciya. "Ban fahimce ki ba mai ke faruwa ne?". Cewar Baseera cikin rashin abin cewa domin gabadaya ta shiga RUƊANI kawai jarumta ce take kokarin sanyawa kanta amma zuciyarta kamar zata faso tayo waje don fargaba. "So nake yi ki bani shawara Baseera na gaji da wannan Bala'in gwanda na san abin yi tun kafin zuciyata ta buga na mace a banza a wofi". Zaro idanu tayi sosai jin abin da take cewa da sauri ta kamo hannunta ta saka cikin nata tana dankewa da wani irin yanayi. "A,a Mariya ki daina fadin haka wannan ba magana bace sam! komai da kika ga ya na faru dake ALKALAMIN ƘADDARAR ki ne a haka ki dauki komai a matsayin JARRABI a rayuwarki kar kiyi gangawar yanke hukunci ki bi komai a sannu karki ji zuciya ta kwashe ki ki zo kina dana sani". Runtse idanu Mariya tayi tana jin zuciyarta na kara ya mutsewa da wani irin mataki tana mikata wani waje na daban buɗe idanunta tayi sosai kan Baseera wanda suka fara kaɗawa. "Hmm Baseera kenan kin fi kowa sanin halin da nake ciki kin fi kowa sanin Bala'o'in da na shiga dole na nemi mafita tun wuri". "Nasan da haka Mariya amma ki saurara ki yi tunani kafin ki yanke hukunci". Sosai take dubanta karo na ba a dadi kallo ne wanda ya sanya Baseera shan jinin jikinta gani take yi kamar Mariya tuhumarta take bisa yanayin da ta lura yak'e ta shiga yi kafun Mariya ta kau da kai daga kallon da take mata ta ja wani numfashi mai tsayi tana tura laɓɓanta cikin baki tana cizawa. "Wa ya dace na zaɓa a cikin su wa kike ganin shine INGANTACCE wanda ya dace da rayuwata?". 'An zo wajan'. Zuciyar Baseera ta fadi tana wani irin dogawa sosai zaka gane firgici a fuskarta idanuwanta a warwaje ta shiga motsa baki tana son yin magana amma ta rasa ta ina zata fara a hankali ta ja hannun Mariya suka koma bakin gadon suka zauna dukkaninsu sai faman ajiyar numfashi suke kamar wadanda suka yi aiki mai wahalar gaske suke zaman hutu. "Kin fasa canza wani saurayin ne daga cikin UKU BALA'In naki?". Baseera ta fadi tana faman sakin murmushin yake gabanta sai dokawa yake so take yi ta dauko gaɓar da zata sanar da Mariya komai amma tana fargaba da tsoro akan abin da zai je ya dawo bata san ya Mariya zata dauki lamarin ba bata san ya zata kalle ta ba anya kuwa ba zata ce ta fiye SON ZUCIYA da son kanta ba? Gyaɗa kai tayi. "Duk mu ajje wannan maganar gefe Baseera na hakura da komai wallahi na mikawa Allah lamarina hukuncin sa kawai naƙe bukata a duk yarda ya zo zan anshe shi". Jin abin da tace ya sanya Baseera dubanta sosai cikin sanya wa kai jarumta duk da dokawar da zuciyarta ke yi. "Nikam nake ganin kamar ki canza zai fi miki lura da yanayin rigimar da kike ciki a yanzu in har kika zabi daya a cikin su kina ganin za a samu maslaha a tsakani kuwa... ko da yake hakan da kike gani shima ya dace tunda ba dukkansu zaki aura ba dole in kika zabi daya dole sauran su yi hakuri tun dake ba MATAR MUTUM UKU bace matar mutum daya ce namiji ne MIJIN MACE HUDU ba ma daya ba". Tunda ta fara maganar take lura da ita sosai kamar akwai wani BOYAYYEN AL'AMARI da take boye mata haka kawai taji ba ta yarda da ita ba sosai take jin haka a jikinta. "Uhmm shikenan tom...ko daya ke ke ma kin kawo shawara amma kuma yanzu in nace zan nemi wani daban me kike tsammanin zai faru?". Murmushi tayi sosai wanda iyakarsa laɓɓan bakinta. "Mazan ne ai ba wuya suke ba sai dai kice nagartarsu ce za ta yi wuya baki san wanda zai zo gareki ba akwai masuyi don Allah akwai kuma masu zuwa da wata manufa ta daban...". Tayi shiru alamun maganar da take bata karasa ta ba numfashi ta ja kafun ta dubi Mariya tana kamo hannunta ta danke cikin nata. "Mariya dama akwai maganar da nake so muyi dake don Allah amma ina so ki dube ni da idon basira kiyi mani kyankyawar fahimta don Allah ba a son raina zaki ji komai ba amma na rasa yarda zan yi ne". Gyaɗa kai Mariya ta shiga yi dama taji ajikinta akwai wani abu a boye. "Yah Tareeq ya jimawa yana kawo min maganarki tun Time din da ya dawo daga School kuka hadu shikenan yake ta faman zarya yana cewa dani wai...". Gaban Mariya yankewa yayi ya fadi lokaci guda ta ji jikinta ya dau ƙyarma amma bata bari hakan yayi tasiri wajan bayyana ba illa murmushin da tayi kokarin daurawa a fuskarta tana karawa Baseera kwarin gwuiwar fadin abin da take son fadi din. "Son ki yake yi Mariya amma ni dai...". Wata irin mikewa tayi gami da fizge hannunta idanuwanta a warwaje ta shiga duban Baseera da tayi mutuwar tsaye kallonta take yi cikin wani irin yanayi bata taba tsammanin maganar da zata yi mata ba kenan bata taba kawo hakan akan taba sosai taji wani iri sosai take jin ta wani mataki wanda ba ta san ya zata kwance kanta ba 'So kuma Yah Tareeq din yake so na?'. ta shiga fadin haka a zuciyarta tana faman girgiza kai idanuwanta na kara rinewa zuwa ja bakin ta na rawa take duban Baseera wacce ita gabadaya a rikice take dama ta san za ayi haka sosai ta san Mariya ba zata dauki wannan lamarin ba domin kuwa an shata ta warke ita kanta ba zata goyi bayan hakan ba duk da dai dan uwa ne kuma za ta so ace Yah Tareeq ya auri Mariya sosai take ganin dacewar haka amma ina! ba damar hakan. A hankali ta shiga ja da baya ta girgiza kai cikin tsananin tashin hankali. "Kiyi Hakuri Baseera don Allah ki yi hakuri ki fahimce ni zuciyata... zuciyata ba zata iya bada wani GURBIN SO ba ta rigaya ta gama so ta rigaya ta gama illatuwa AKAN SO ko nace miki zan sake so to nayi miki karya kiyi hakuri ba zan iya ba". Tana gama fadin haka tayi hanyar ficewa da sauri kanta take ji yana wani irin sarawa gabadaya taji duniyar na juya mata a haka har ta sauka Allah ya taimake ta ba kowa a falon cikin hanzari ta fice daga cikin gidan baki daya ta dauki hanya sai faman zancen zuci take yi kamar waya zararriya. Ita kuwa Baseera hada kai tayi da gwuiwa tana jin yarda zuciyarta take zafi sosai bata so yin wannan maganar ba dama can abin da zai faruwa take guda bata son abin da zai bata kawancensu akan Yah Tareeq ba yarda bata yi dashi ba amma yaki yarda yanzu ya zama dole ta fada masa gaskiya duk da yana dan'uwanta ba za ta so abin da zai cutar da Mariya duk da itama tana kwadayin yayan nata ya auri Mariya amma lokaci ya kure ba damar yin haka din. ***** Tafiya kawai take tana saka kafarta duk inda ta sauka ba ta tsaya neman abin hawa ba domin bata da wannan natsuwar Allah ya taimaketa har ta isa unguwarta. Kallo daya zakayi mata ka gane bata cikin natsuwar sam! Cikin wannan yanayin ta iso layin su har zuwa wannan lokacin bata dawo hayyacin ta ba kamar daga sama taji ta bangaji abu mai girma hakan ya sanyata yin baya luuuu tana kokarin faduwa runtse idanu tayi sosai tana jiran jin ta a kasa amma sai akasin haka rikota taji anyi sosai an dagota wani irin Shock taji jikinta ya dauka ya mikawa kwanyarta da zuciyarta lokaci guda suka tsaya cak! da aiki. A hankali ta shiga kokarin buɗe idanuwanta zuciyarta na dawowa hayyacinta tana bugawa fargabarta daya Allah yasa ba wani ta buge ba zai hukunta ta... Bata gama tunanin ba ta ji gabanta ya yanke ya fadi lokacin da idanuwanta suka buɗe akan fuskarsa kallon shi ta shiga yi shima kallonta yake yi da tattausar murmushi a fuskarsa gabadaya taji ta a wani irin yanayi jikinta sai ansa wani bakon al'amari yake yi bata yi kokarin kwace kanta ba domin ji tayi gabobin ta gabadaya kamar sun daina aiki motsi ma ta kasa yi. Runtse idanu tayi sannan ta buɗe izuwa lokacin ta fara gano komai dake faruwa da sauri ta kwace kanta daga gareshi tana ja da baya idanuwanta har zuwa lokacin ba su bar cikin nasa ba sai faman ajiyar numfashi take yi mai girman gaske. Sosai ya fita shiga cikin yanayi mai girman gaske zuciyarsa yake ji tana dokawa da wani irin yanayi zuciyar na kara buɗewa sosai idanuwansa suna dauko masa wasu abubuwa masu muhimmanci daga idanuwanta suna sauke wa akan sa. A jiyar zuciya yayi murmushi na kufce masa a fuska kafun ya kau da kai zuciyarsa na kara saurin bugu ita kam gabadaya ta gama tafiya wani mataki da sauri ta fara daga kafafuwanta da take ji suna kokarin lauyewa su zubda ita kasa a haka har ta zo gilma shi. "MARIYA!". Ya fadi da sauti tsayawa tayi cak! zuciyarta na bugawa kafun ta dubeshi na yan sakanni sannan ta ja jiki ta bar wajan cikin hanzari domin bazata iya tsayuwa ba ta tabbata in tajima a haka sai dai a tsince ta zube a kasa tana jin zuciyarta na kara buɗewa da lamarin Dr.Karami bata san mai yasa haka ba sosai take jin GURBIN SON da ta bashi a zuciyarta yana kara buɗewa yana kara fadi yana saukar da wasu lamuraka masu taushi a cikin zuciyar ta ta... *_KAMALA MINNA_*😘😘😘 [9/24, 9:15 AM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA HAMSIN. A hankali take duban Hajiya Layla gabanta na sake tsananta faduwa duban mutumin dake zaune gefe guda tayi sannan ta kalli dubun nan kudin da suke ajje cikin leda wani irin kartawa taji zuciyarta tayi da wani irin yanayi mai zafi da raɗaɗi ji take yi kamar ta hadiyi zuciya ta mace. Sosai ta ke jin komai na canza mata sosai take jin zuciyarta na sake yayyagewa da tashin hankali wanda bata yi tsammani zata kasa daukarshi ba tayi tunanin zuciyarta zata bata dama har ta ga kullewar wannan lamarin amma ina! ba zata iya ba da sauri ta fara ja da baya idanuwanta na rinewa da tashin hankali kafun ta juya da gudu tayi cikin dakinta. Hajiya Layla da tun dazu take kallon Areefa zuciyarta na tausayinta ta sani tabbas dole Areefa taji ba dadi amma ba yarda zatayi dole wannan hanyar ta kasance mafita a gareshi su ita ce kawai take hango komai zai zama daidai bata tare da an samu matsala ba nisawa tayi sannan ta dube shi da fuska cikin damuwa. "Yanzu ya kukayi da su mutanan da suka zo neman Aure?". Murmushi ya saki tare da gyara zama sosai yana fuskartarta kafun ya ja numfashi. "Ai Hajiya ba wata matsala duk yarda kika ce ayi haka akayi sati biyun nan dai masu zuwa za a daura auren kamar yarda kika bukata su ma ba su ja ba". Murmushi tayi wanda iyakarsa laɓɓan bakin ta kafun ta janyo jakarta dake gefe ta zuge zip din kudi ta zaro ta mika masa kafun tace. "Ga wannan sai ku fara saye-saye wanda ka san gidan biki na bukata sannan duk wani abu zan turo muku dashi wanda zai tabbatar da cewa eh bikin na gaske ne". Gyaɗa kai yayi yana ansar kudin goɗiya yashiga zabga mata kafun ya mike ya fice daga cikin gidan. Sai lokacin Hajiya Layla ta samu tayi ajiyar zuciya mai karfi a hankali ta mike ta dauki ledar da kudin suke ciki zuciyarta na mikata wani mataki na tausayin Areefa a haka har ta isa cikin dakin ruf! da ciki ta hangeta ta hade fuskarta da filo a hankali ta taka ta isa gareta bakin gadon ta zauna bayan ta ajje kudin gefe guda. Duban Areefa ta shiga yi wacce ta tabbatar taji shigowarta a hankali ta kai hannunta saitin bayan ta tana bubbugawa kadan-kadan kafun ta shiga cewa. "Areefa mai yasa zaki yi mani haka bayan kin min alkawarin ba zaki sake nuna wani damuwa kan lamarin nan ba karki manta ba wai nayi niyyar yin wannan abun bane don cutar dake a,a nayi ne don ƙwatar miki yancin ki wanda na tabbata in komai ya kammala ke akaran kanki zaki yi farin cikin haka". A hankali Areefa ta dago tana zama idanuwanta sun kaɗa sun yi jajir sai faman cizon laɓɓa take tana dakune fuska. "Farin ciki fa kika ce Maama kina tunanin a duniyar nan zan sake samun farinciki ne kina tunanin farincikin da ya guje mani zai sake dawowa gareni ne a filin rayuwar ta bana tsammanin haka zai kasance na sani rayuwata ba komai bane a duniyar nan bana tunanin a rayuwata farinciki zai wanzu...". Numfashi taja da taji yana sarke mata wasu kwalla masu zafin gaske suka zubo mata saman kuncinta hannu ta saka ta dauke su kafun ta shiga girgiza kai. "Ban san ya zan fuskanci wannan rayuwar ba kawai ina yin ta ne ba wai don farinciki ko kwanciyar hankali ba dama can Allah ya halicce ni a haka zan kare rayuwa ta cikin kunci da takaici da rashin 'yanci na lura a duniyar nan in har baka da makusanci to kai ba ka da wata daraja ko kima da za a ganka da ita kai da banza duk daya ne....Maraya shima mutum ne kamar kowa yana da 'yanci a wajan ubangijinsa ko bai dashi a idon jama'ar duniya bani nayi wa kaina haka ba ba a son raina na zo a wannan yanayin ba amma saboda rashin 'yanci da sanin daraja ta aka lalata min rayuwata aka kashe mani duk wani hanyar da zan samu kwanciyar hankali da natsuwa Maami kina tunanin ko na auri Dr.Erena na fita akwai wanda zai aure ni a yarda nake ne?". Girgiza kai ta shiga yi kukanta na daduwa hawaye sai sintiri suke mata zuciyarta take ji ta matsewa da wani irin ciwo mai girman haske abun da ya faru da ita shekaru masu auki can baya take hangowa kamar yanzu komai yake faruwa runtse idanu tayi tana sanya hannayenta saman kirjinta da take jin yana barazanar tarwatsewa. Ita kanta Hajiya Layla hawaye take yi ji take yi kamar yanzu ta tsinci Areefa cikin wannan mawuyacin halin janyo Areefa tayi jikinta ta shiga rarrashin ta hakan ya kara tsananta kuka Areefa sai da tayi mai isarta ba tare da Hajiya Layla ta hana ta ba domin ta san dole taji rashin jindadi dole taji kunci da bakinciki ba 'ya macen da zata so aci zarafin ta haka ba 'ya macen da za ta samu kwanciyar hankali a irin wannan halin. "kiyi hakuri Areefa kiyi hakuri komai zai wuce ba wai zaki yi wannan auren don ke kadai ba ne Areefa duba zaki yi da halin wannan mutumin in har aka barshi a doran duniyar nan Allah kadai ya san iya yarda zai tsaya da cutar da mutane hanyar daya ce shi ne ki aure shi na tabbata ke sai kin yi mamaki abin da zai faru ba dai shi yace yana son ki ba to wallahi tallahi ya janyo wa kansa duk wani kunci duniya da bala'i da yake saka mutane sai ya ji yarda ake jin sa ni dai kawai ki bani lokaci ki ajje komai a gefe sannan ki cigaba da addu'a da izinin Allah sai munyi nasara akan sa". Dago jajayen idanuwanta tayi tana mai ajiyar numfashi zuciyarta sai faman kartawa take yi. "Shikenan Maama komai ya wuce zan yi yarda kike so". Murmushin dole Hajiya Layla ta saki tana sake rungume Areefa tana jin yarda zuciyarta ke bugawa da sauri-sauri hakan ya kara mata jin tausayin Areefa dole ta kwatar mata yanci ta dole ta nunawa Dr.Erena a duniyar nan ba komai yake tabbata ba musamman zalunci da cin amana sai ta nuna masa komai da yake yi akwai karshen sa kuma sai ta tabbatar masa MARAYA shima mutum ne kamar kowa yana da daraja da kima. **** Kallo daya zaka yi mata ka gane irin ramar da ta zabga cikin yan kwanaki gabaya ta kasa kwantar da hankalin kullum cikin tunani da damuwa take akan abin da zai je ya dawo tsakaninta da Dr.Erena sosai take fargaba da tsoro sosai take jin wani irin yanayi a jikinta komai take ji yana sauya mata ji take yi kamar ba ita ba ba ta san ya wannan lamarin zai kasance ba bata san mai yasa Hajiya Layla take son bikin nan ya tabbata ba taki fada mata dalilinta tace ba yanzu ba hakan na kara sanyata cikin damuwa. A hankali take tuki zuciyarta na ta faman safa da marwa har ta isa kofar gida tayi parking sannan ta fito hannunta rike da manyan ledoji da alamun sayayya tayi haka kawai take ji yau gabanta na faduwa ta rasa dalili ko da yake ba zata ce ta rasa dalili ba in ta danganta da lamarin nan lamarin dake kokarin faruwa da ita tana cikin wannan tunanin ta ji wayarta ta fara Ring runtse idanu tayi kafun ta dubi fuskar wayar dake hannunta ganin mai kiran ya sanyata jan dogon tsaki kamar zata tsinke harshenta sai da tayi kamar ba zata dauka ba amma tuno maganar Hajiya Layla da take cewa karta sake ta nuna hanyar daya da zai fuskanci wani abu ta nuna masa kulawa sosai musamman a daidai irin wannan lokaci da bikin ya gabato saura mako daya. A hankali ta kai wayar kunnnan bayan yayi kira na biyar bata daga ba numfashi ta ja ba tare da ta ce dashi kala ba shi kuwa acan nashi bangaren jin ta daga wayar ya sanya shi sakin ajiyar zuciya tare da murmushi. "Amarya bakya laifi ko kin kashe dan masu gida". Abin da ya fadi kenan cike da tsokana yana faman dariya ita kuwa Areefa ji tayi kamar ta kurma ihu don bakin ciki da takaici haka kawai taji wani kululun wani abu mai girman gaske ya tokare mata zuciya numfashi ma na kokarin gagararta ja runtse idanu tayi tana jin yarda kanta ke sarawa kamar zai rabe gida biyu a hankali ta ciji laɓɓanta kamar zata bula su kafun ta sake jan numfashi mai tafe da makakin takaici da bakin ciki. "Uhmm aiko wannan maganar taka ba gaskiya bane domin in har na kashe d'an mai gida ba abin da zai hana ba a hukuntan ni ba wannan falsafar taka sam bata yi ba". Ta fadi da nuna kulawa amma a filin zuciyarta da fuskarta wani kunci ne yake kokarin kashe ta. Wata mahaukaciyar dariya ya saki mai sauti kamar zai tarwatsa mata kunne da sauri ta zare wayar tana mai sakin numfashi kallon wayar take yi a wani irin yanayi ji take yi kamar ta rotsata da kasa ko ta samu natsuwa ko yaya take a zuciyarta. "Ai ke ta daban ce ko a cikin matayen ko kin kashe ba wanda ya isa ya hukunta ki". Ta jiyo sautin muryarsa na fadin haka runtse idanu tayi a zuciyarta tana mai cewa 'kenan ce masa akayi kowama mara imani ne a duniyar sa kaico'. Amma a fili mai da wayar tayi kunnnanta tana murmushin da yafi yak'e ciwo. "Uhmm ka ji ka da wani batu lokacin da zaka kira jami'an tsaro suyi ram dani ai duk wannan batun mantawa zakayi dashi". "Wai kina zaton ba zan iya bane Areefa?". Ya fadi cikin iyakar gaskiyarsa bata yi mamaki ba don ta san kadan daga aikin sa ne dakune fuska tayi kafun tace dashi. "Ina zuwa gida zan shiga yanzu kaji sai an jima". Tana fadin haka ta kashe wayarta tana jin yana magana amma taki kula shi tsaki ta ja kafun ta rangwadar da kai cikin yanayi na fidda tsammani zuciyarta na kara tsanar halin Dr.Erena tsoro take yi akan abin da zai je ya dawo. Da wannan tunanin ta karasa cikin gida zuciyar cike da yarda al'amarin nan zai kasance. Haka rayuwar tayi ta tafiya zuciyarta Areefa na kara rikicewa da al'amarin Dr.Erena don ta ga dai da gaske yake an kawo lefe da komai da komai ranar daurin aure kawai ake ji izuwa lokacin gabadaya ta gama fidda tsammani Hajiya Layla ce take ta faman tausarta tana bata baki amma ina lokuta da yawa zama take yi ta ci kukanta har ta koshi ba abin da ta tsana kamar wai ita ce zata auri Dr.Erena mutumin da ya bata mata rayuwa yayi mata illa ya hana ta duk wani farin ciki ya wulakanta ta wai shine a matsayinta kaicon wannan rayuwa kaicon wannan rana da ta zo a gareta mutumin da ta tsana tsana mai tsanani a rayuwarta shine za su hada inuwa daya a haka ta cigaba da dakon kiyayyar Dr.Erena har zuwa ranar da Aure ya tabbata akan su bayan an yi shagulgula wanda hankali ba zai dauka ba an kashe kudi bidi'o'i ba kalar da ba ayi ba Areefa tayi kuka kuka mai ansa suna kuka a ranar ta so Allah ya dauki ranta ta so ta mutu da ganin wannan BAKAR RANA a rayuwarta kunci da bakin ciki a ranar ya kara daduwa a gareta haka ta wuni cur tun da aka ce an daura auren wani zazzafar zazzabi ya saukar mata ta shiga rawar sanyi kamar wacce aka saka cikin firji aka fiddo ta numfashin ta sai sauri-sauri yake yi ita kanta Hajiya Layla sai da ta firgita da yanayin da ta ga Areefa a ciki a wannan halin haka ta dauke ba tare da sanin kowa ba ta kaita asibiti nan aka ba su gado sai da ta sha ledar ruwa biyu tare da allurai sannan bayan jikin ya lafa suka dawo gida Hajiya Layla ta yi kuka ita kanta sannan ta shiga bata baki akan cewa tayi hakuri ba abin da zai faru da ita da izinin Allah Dr.Erena ba zai taba nasara akan su ba sosai ta bata baki har zuwa dare lokacin da za a kai amarya motoci kuwa ba a maganar su jerin gwano sukayi da kyar da suɗin goshi sannan Areefa ta yarda aka fiddo da ita daga cikin gidan bayan Hajiya Layla ta bar gidan domin cewa tayi ba zata iya tsayawa ba tana tsoron abin da zai faru tausayin Areefa zai iya hana ta cimma burinta. Tunda aka saka Areefa cikin motarta da sauran mutane da Hajiya Layla ta dauki hanyar su yan kai Amarya shikenan ta tsagaita da kuka zuciyarta na dauko mata wani tunani tana kawo mata tsanar Dr.Erena da kiyayyarsa na kara hauhauwa a zuciyarta abin da take gudu shi take jin zuciyarta na kokarin bata damar aikatawa sosai ta aminta da wannan shawara lokaci guda duk wani fargaba da tsoro suka fice mata har lokacin da suka isa katafaren kerarren gidan da za a sakata wanda ya gama haduwa tsayawa fasalta shi ma kauyanci ne babu abin da babu a cikin sa sai babu din sai dai ga Areefa duk wannan bai yi mata ba tana jin yan kai amarya na zuzutawa da koɗawa da cewa tayi goshi ta samu aljanar duniya amma ita a wajanta ko gidan yari yafi mata da wannan bakin gidan... *_KAMALA MINNA_*😘😘😘 UKU BALA'I NA KAMALA MINNA BABI NA HAMSIN DA DAYA. Sosai Baffa ke kallon yanayin cikin takaici da tsananin mamaki abin da bai taba zato ko tsammani ko a mafarkinsa bai yi tsammanin zai sake tuna shuɗaɗɗen wannan lamarin ba amma bisa akasi wai yau Bello ne a gabansa shi ya tsinta shine har yayi masa magani kaico mutumin da ya tsana tsana mai ansa suna tsana a filin duniyar nan bai taba tsanar wani bawa kamar Bello ba amma wai yau shi ne a gidan sa yake zaune har yake tattalin sa yake kula masa da rayuwa ya ajje komai nashi ya bata lokacin sa mai tsayi wajan bautawa wanda ya tsana a filin duniyar nan kaico. Wani irin maƙaki ne na takaici yake ji yana tunkodo masa zuciya ji yake yi ko wani sashi na zuciyarsa da ruhinsa suna shiga wani halin kunci mai tsanani. Kai kawo kawai yake yi cikin dakin zuciyarsa na tunzurashi tana tuno masa da abin da ya faru sama da shekaru ashirin wanda ya ɗaɗe da binne wa ransa ba zai taba waiwaye ba amma yau rana daya ciwon da ke cin zuciyarsa ya tashi. Runtse idanu yayi ji yake yi kamar ya kurma ihu don takaici da bakin ciki bai san ya zai yi ba bai san abin da zai yi wa Bello domin daukar fansa ba zuciyarsa ta shiga tunkodarsa akan ya dauki hukunci mai girma akansa wanda zai warkar masa da ciwon da ya haifarsa ba ma wannan ba 'yarsa yake tunawa 'yarsa mai biyayya a gareshi amma AKAN SO ta ajje duk wani girmamawa da biyayya da take masa ta shiga yiwa so biyayya ta rabu dashi ta rabu da kowa nata ta guje su duk akan so ya yafe ta tuni ya yafe ta cikin zuri'arsa ya sallamawa duniya ita amma yau daya yaji zuciyarsa na tuno masa da zaman da yayi da ita da kyautatawa da take masa. Numfashi yaja mai karfi idanuwansa lokaci guda suka kawo kwalla komai ya faru dashi a filin duniyar nan Bello ne Sanadi ya raba shi da inda ya zauna zaman shekaru masu yawa ya rabashi da farin ciki ya raba shi da 'yarsa duk wani tashin hankali da kuncin rayuwa da suka shiga shine sila komai ya faru da su shine sila. Dafe kan sa yayi zuciyarsa na kara rura wutar kiyayyar da yake yi masa ji yake yi kamar ya kashe shi abin da zuciyarsa take sanar dashi kenan amma yana gudun haka tunanin 'yarsa yake yau daya ya tuna da ita yau daya yana son ganinta bai san a wani hali take a yanzu ba bai sani ba ko tana raye a duniyar nan ko ta mutu duk bai sani ba ansar tana wajan Bello wanda shi kuma a duniyar ba wanda ya tsana ya sake gani kamar shi. A hankali ya fara jan kafafuwansa da sukayi rauni sosai gabadaya jikinsa ya saki sosai tafiya yake yi yana bin kowa da kallo har lokacin da ya isa in da ya baro Bello zaune bayan ya gama fahimtar wanene shi tun daga nesa yake hangen sa yana jin yarda zuciyarsa ke kara narkewa da bakin ciki da Bello ya zama sila ji yake yi kamar yana isa ya dauke shi da mari. A wajan Bello abin da yake ta nazari kenan akan Baffa sosai ya shiga tashin hankali sosai ya shiga cikin firgici da razana sosai yake hango yarda Baffa zai dauke shi da irin hukuncin da zai yi masa in ya gane shi wanene lokaci guda zuciyarsa ta karya ba wanda yake tausayi sai matarsa ya sani komai ya faru da ita shine sila AKAN SO komai ya faru a tsakanin su domin tayi wa so biyayya ta rabu da komawa nata tace sai shi sosai kalamanta suke masa yawo kai a can lokacin baya bayan iyayenta sun sallamata gareshi sunyafe ta gareshi... "Bello kai kadai nake dashi a duniyar nan kai ne gata na kai ne komai nawa saboda so na rabu da kowa saboda so na rabu da komai nawa don Allah ka rikeni da amana karka sa nayi kuka A DALILIN ƊA NAMIJI ina tsoro...ina tsoron abin da zai je ya dawo Bello in har ka ci amanata ka tabbata ba zan taba yafe maka ba ni kaina ba zan yafewa kai na ba na roke ka". Wani hawaye ne suka gangararo masa lokacin da ya tuno kalamanta tana zubda hawaye cikin tsananin firgici da yanke tsammani komai na rayuwa sai BIYAYYAR SO da take tsammanin tayi kuma take tsammanin zata samu kulawa akan wanda tayi wa so din. Saukar hucin da yaji ne akan sa ya sanya shi saurin dawowa hayyacin sa yana waigawa Baffa ya gani fuskarsa ta haɗe kamar bakin hadari idanuwansa sun kaɗa sun yi jajir sai faman hirji yake yi kamar wanda zai ci babu shi kan sa Bello ya tsorata da yanayin da ya gan shi a ciki. Zuciyarsa ce ta shiga bugawa da sauri-sauri kamar zata faso kirjinsa ta fito saboda tsananin firgita ba abin da yake hangowa cikin idanun Baffa sai kiyayya da rashin so kallon da yake yi masa na tsana da takaicin ganin sa sosai yake tuno waye Baffa sosai yake tuno irin DAMBARWAR da suka kwasa a tsakaninsu akan ya rabu masa da 'ya har fada Baffa ya ja shi suyi ya sha jibgarsa ya sha yi masa rotse da sanda amma duk wannan bai saka ya guje 'yar sa ba sosai yake hango irin ikirarin da Baffa yayi a ranar da ya sallama Habeeba gareashi a ranar da aka daura mata aure a ranar da suka kwashe komai na su suka bar garin. "Ba zan taba yafe maka ba Bello ka cuce ni ka dasa min ciwo a zuciya mai girman gaske amma ka sani wallahi wallahi kaji na rantse zan sallama maka Habeeba ka je ka aure ta amma ka tabbata babu ni babu ku har abada bana kaunar na sake haduwa da daya daga cikin ku". Runtse Idanu Bello yayi jin zantukan Baffa suna maimaita kan su a cikin kwanyarsa tsoro na kara ziyartarsa sosai a zuciya ya sani Baffa ba zai taba kyaleshi ba ya sani dole ya dau hukunci akan sa tun da yau ALKALAMIN ƘADDARA ya hada su har suka zauna waje daya a lokaci mai tsayi wanda shi a akaran kansa ba zai iya cewa ga adadin lokacin da ya kwashe a tare da su ba. Kawai ji yayi tum akasa da sauri ya waigo Baffa ya gani ya fadi yana faman numfarfashi kamar wanda rai ke kokarin fita daga jikinsa zaro idanu yayi sosai cikin tsananin firgici ya isa gareshi yana kokarin tallabo shi amma duk da halin da Baffa yake ciki bai hana shi kokarin janye jiki daga gareshi ba hakan ya kara rikita Bello sakin baki yayi yana kallonsa gabansa na tsananta bugawa. A daidai lokacin su Iro suka dawo daga kiwo ganin abin da ke faruwa da gudu suka iso suna kiran sunan Baffa Ja'e ya rungumo shi yana mai duban Bello da hawaye suka balle masa suna ta kwarara kamar wani karamin yaro. "Na...ts.a..na she bana...son...ganinsa". Cikin sarkewar muryar Bafffa yake fadin haka da sauri suka shiga duban sa domin ba su gane in da ya dosa ba ba su gane mai yake nufi da kalmar da yake fadi ba sosai suka rikice suka shiga kokarin daukarsa domin kai shi daki amma idanuwansa na kan Bello da yayi kasa ke yana kallon ikon Allah iya tashin hankali ya shiga a wannan lokaci zuciyarsa sai faman zillo take tsoro yake yi kar ya zama ajalin Baffa don ya lura yanayinsa ya tabbatar ya gane ko shi waye da sauri ya mike ya bi bayan su daidai bunkar da suka shigar da Baffa ya tsaya tsoron shiga yake don bai san abin da zai faru ba ya sani Baffa ya tsane shi in da ya san ko shi waye tun farko ba zai dube shi har ya taimaka masa ba. A cikin Bunkar kuwa kokarin taimakawa Baffa sukayi har ya fara dawowa hayyacin sa sai faman magana yake saki wanda su dukkansu ba su gane abin da yake nufi ba idanuwansa sun kara kaɗewa sosai. "Bana son na sake hade idanuna dashi bana kaunarsa na tsane shi ku fitar min dashi daga cikin zuri'a annoba ne shi bala'i ne komai da ya faru dani shine sila shi ne ya dasa min ciwo mai girma a zuciya shi ya raba ni da farinciki na a dalilin sa na rasa matata a ta dalilinsa ne komai nawa ya kasance da kunci a cikinsa". Magana yake yi idanuwansa na kawo hawaye suna zuba sosai su Ja'e suka firgita da ganin tsohon na su cikin wannan yanayin abin da ba su taba gani ba kenan tsayin rayuwarsu kukan mahaifin su lokaci guda suma zuciyoyinsu suka karye kwalla ta cika masu idanu Iro ne yayi kokarin duban Baffa a dan firgice. "Baffa wai me ke faruwa ne me ya same ka kuma waye kake cewa ka tsana?". Runtse idanu Baffa yayi zuciyarsa na zafi kafun ya buɗe su yana duban su daya bayan daya yana faman ajiyar zuciya. "Mutumin da na taimakawa mutumin dana bata lokaci na ina jigilar ganin yana dawo mutum mutumin da na shafe tsayin lokaci ina jinya mutumin da duk na wahala akan shi ashe ban sani ba mikiyi nane ashe ban sani ba annoba ne annobar da ta lalata komai nawa ta hanani farinciki tana hanani kwanciyar hankali ta raba ni da masauki dana kwashe shekaru ni da zuri'ata amma a ta dalilinsa na bar komai na dawo nan da zauna". Duban junansu sukayi kafun su sake duban Baffa cikin rashin fahimtar maganganunsa murmushi mai ciwo ya saki kafun ya dauke hawayen da suka zubo masa nan ya shiga ba su labarin komai dake faruwa wanda ba su sani ba don lokaci ba su wuce shekara biyu ba. Mamaki sosai ya cika su lokacin da ya gama ba su labari duban sa suka shiga yi cike da mamaki da al'ajabin lamarin domin duk wannan lamarin ba su san dashi ba Ja'e ya kokarta duban Baffa cikin yanayi na tausayi. "Amma Baffa kana ganin wannan matakin daka dauka shi ne daidai?". Wani irin duba Baffa yayi masa kafun yaja numfashi. "Me kake nufi Ja'e? Kana nufin hakan da nayi ba daidai bane ko me?". Girgiza kai ya shiga yi cikin kunar zuci sosai yake jin takaicin lamarin da kuma haushin Bello. "Ba wai nace baka kyauta bane amma kana tunanin abin da kayi wa Yayah Habeeba daidai...". "Dakata min Ja'e me kake son sanar dani kana nufin ban yi mata adalci ba ko me kasan Allah ko ita ce 'YA DAYA TAK! dana haife zan iya rabuwa da ita tunda har ta fifita wani a kai na balle kuma ina da wasu 'ya'ya mahaifiyarku da sunan Habeeba ta mutu a bakinta tun lokacin da muka baro inda muka ta so shikenan ta rasa kwanciyar hankalinta har zuwa lokacin da ta rasu ta yaya kake zaton zan yafe ko zan dauki lamarin da sauki". Ya karashe cikin zafin rai da tsananin fushi mikewa yayi cikin hanzari yayi waje Bello na tsaye kikam tun dazu zuciyarsa da kwanyarsa duk sun tsaya cak! da aiki ya rasa mai ke yi masa dadi saukar duka yaji da sanda a tsakar kai hakan yayi matukar firgita shi Baffa ya hango sai faman Hirji yake yi bai ankara ba ji dumin jini na sauko masa zuwa fuska duban Baffa yake yi cikin wani irin yanayi yana hango kiyayyar da yake yi masa a karo na biyu yana daga sandar yana kokarin sauke masa da sauri Ja'e ya rike wanda ya fito a daidai lokacin ya shiga duban Baffa yana duban Bello dake tsaye jini duk ya wanke masa fuska lokaci guda. Wani irin duba Baffa yayi masa kafun ya fizge sandar yana nuna Bello da ita. "Tun wuri ka fice mani daga cikin ruga tun kafin nayi ajalinka na fada maka dama duk ranar da muka sake haduwa da juna sai na yi ajalin ka don haka tun kafin na kashe ka na mai da kai in da na tsinto ka ka san in da dare yayi maka". Sake duban Baffa yayi zuciyarsa na zafi da raɗaɗi a hankali ya shiga takowa yana iso wa gareshi da sauri Baffa ya daga sandar jira kawai yake ya iso ya dauke masa a jikinsa sai faman ɓari yake yi kamar wanda ya sha dukan ruwa su Iro kam lamarin ya fara shallake tunanin su ba su taba zaton haka Baffa yake ba ba su taba zaton yana da zuciya haka ba tunda suke dashi ba su taba ganin ya aikata makamancin wannan halin ba gani suke yi kamar a mafarki ba gaske ba. "Na tsane ka karka sake ka iso inda nake wallahi zan yi ajalinka". Duk ikirarin da Baffa yake yi bai hana Bello isowa gareshi ba haka shima Baffa yana isowa ya sauke masa sandar a tsakar kansa wanda tayi sanadiyar zubewarsa kasa warwas sumamme da gudu su Ja'e sukayi kansa shi kuwa Baffa jikinsa ɓari kawai yake yi gaɓadaya ya shiga wani yanayi na rashin hayyaci. [10/4, 10:25 AM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU-BALA'I NA KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA HAMSIN DA UKU. *_My Kawa Amra ina tayaki murnar kammala labarin ki mai taken AMRAH NAKE SO Allah ya amfani al'umma da ilmin da kika nuna a ciki da fadakarwa ya kara miki basira da hazaka....Makarantar Uku bala'i yasin laifin Amrah ne da kuka jini shiru 2days kurciya tayi mani_*😁 *_Milk Candy Happy Bizday Allah ya karo shekaru masu amfani ya inganta rayuwa sai mun zo cin Cake_*😁😁😁 haka kawai taji zuciyarta na tashi kamar wanda taci abun da ranta bai so ba tunda aka kawo ta cikin gidan Dr.Erena gabadaya ta rasa gane kanta sosai take jin zuciyarta na raɗaɗi da zafi ga wani kunci mai girma da take jin yana ta faman kai kawo a ko ina na zuciyarta da ruhinta. Numfashi take faman saukewa kamar wacce tayi gudun fanfalaki a hankali ta sauko daga kan gadon jikinta sanye da wando da riga wanda suka kamata sosai bayan su ga rigar barci da ta sanya a sama sannan ta daura zani akai duk wannan abin da tayi ta yi ne saboda kar Dr.Erena ya shigo mata daki duk da ta kargame da key amma duk hakan bai kwantar mata da hankali ba barci ma gagararta yayi a hankali ta shiga takawa har ta isa toilat din tayi abin da zata yi ta fito haka kawai take ji wani iri gabadaya ga wani kamshi da take shaka yana tayar mata da zuciya tun ranar da aka kawota gidannan take jin haka amma ta rasa dalili isa kofar dakin tayi ta buɗe da key sannan ta leka ganin ba kowa ya sanyata sakin ajiyar zuciya ta nufi F falon gidan a hankali tana dube dube cikin yanayi na dan tsoro don bazata manta arangamar da tayi da Dr.Erena aa a daren ta na farko inda suka kwashi rigima tun ranar bata haduwa dashi ba sai dai taji shigowarsa da fitarsa amma ko sau daya bata taba gangancin fitowa yana gida ba. Tunda ta tunkaro falon take jin warin na daɗuwa sosai har sai da ta toshe hancinta sosai ta shiga zare idanu gabanta na tsananta bugawa yawatawa da idanuwanta ta shiga yi cikin falon amma bata ga kowa ba hakan ya bata mamaki matuka cikin yanayi na tsoro da fargaba ta tsaya tsakiyar falon tana dube dube sam bata lura da mutumin dake kwance saman kujera ba bata san ya taso ba sai dai kawai taji an danko mata kugu wata irin razananniyar kara ta saki tare da toshe hancinta da take jin warin ya dadu nan ta shiga kiciniyar kwatar kanta amma ina rikon da yayi mata ba na wasa bane ji tayi kamar zata mutu numfashinta sai faman fizga yake yi runtse idanu tayi gami da yin wani yinkuri sosai taji karfi ya zo mata wanda bata san tana dashi ba ta fizge kanta ta daka tsalle can gefe guda sai faman numfarfashi take yi. Kallo ta bishi dashi da idanuwanta da suka gama razana da tsoro sosai ta firgita da yanayinsa gani take kamar ba Dr.Erena da ta sani ba gabadaya ya canza suffarsa take ganin tana riketa mata kamar ba nashi ba da sauri-sauri ta shiga ja da baya kafun lokaci guda ta kwasa da gudu tayi dakinta ta mai da kofa ta rufe zamewa tayi ta zauna jikin kofar ta runtse idanu cikin wani irin yanayi zuciyarta sai zillo take yi kamar zata faso kirjinta ta fito. Ta dauki lokaci mai tsayi a wajan zuciyarta da kwanyarta sai kai kawo suke yi mamaki take yi yarda take jin warin nan da ya jima tana jinsa bata taba zaton a jikinsa yake ba sai yau Allah kawai ya kwaceta amma ta tabbata in ba don haka ba da tuni ta mutu don sosai take jin warin na ratsa mata hanci yana samun masauki a cikinta. Wani kuka ta saki mai ciwo ita kam! taga ta kanta ba ta san kaddarar da ta jayota wannan gidan ba bata san mai yasa tayi wannan AUREN ƘADDARA din ba ita kam bata ga amfanin wannan auren gareta ba illa bala'i da zai jaza mata. ***** Abu kamar wasa Gabadaya Areefa ta rasa gane kanta tun ranar da wannan lamarin ya faru tsakaninta da Dr.Erena sosai ta firgita yau kimanin wataninta biyu kenan a gidansa amma ta rasa kwamciyar hankali da natsuwa. "Maama don Girman Allah ki zo ki fiddo ni daga cikin wannan gidan zan mutu". Cewar Areefa a wani talatin dare da tayi wani mugun mafarki da yayi matukar tsorata ta. "Wai me ke damunki ne Areefa eyee ba na ce miki ina nan zuwa ba amma kin ki kwatar da hankalinki ki natsu mana ina nan zuwa gobe da safe". Wani kuka ta sake rushewa dashi matsanancin sai faman zarya take yi a tsakiyar dakin daga ita sai kayan barci kanta duk a hargitse kamar sabuwar mahaukaci. "Allah Maama mutuwa zanyi ba zan iya jira har gobe da safe ba don Allah ki zo ki fiddo ni daga bakin gidan nan...". Bata karasa maganar da take yi ba taji an hau dukar kofar dakin nata kamar za a karyata wani tsalle tayi ta ɗane saman gado idanu a warwaje. "Maama kina ji ko kin gan shi nan fa ya zo yana dukar min kofa wayyo Allah na zai kashe ni". "Innalillahi wa inna ilaihr raji'un". Hajiya Layla ta fadi cikin sauti don tana jiyo sautin bugun kofar da ake yi sosai ta firgita ita kanta ta fara tsorata da yanayin da take jin Areefa a ciki sosai take fargarbar abin da zai je ya dawo kai kawo kawai take yi tsakiyar falon tun lokacin da Areefa ta bugo mata waya tana kuka gabadaya ta fice hayyacinta bata son abin da zai cutar da Areefa bata so a kuma yin na biyu bata so ace ta dalilinta Areefa take fadawa cikin kunci da bala'in rayuwa. Hannayenta ta saka ta dafe kanta tana jin yarda yake juya mata a hankali ta ja kafafuwanta da take jin sun yi mata nauyi sosai ta zauna bakin kujera jikinta sosai yake rawa. "Areefa kina jina". Ta fadi cikin kwantacciyar murya mai cike da rarrashi. "Ina jinki Maama ni dai don Allah ki zo ki fidda ni daga cikin gidan nan na roke ki". Ta fadi tana mai sake rushewa da kuka a daidai lokacin kuma ya balla kofar ya shigo habawa ba ta san lokacin da tayi cilli da wayar ba ta yi hanyar toilet da gudu tana shiga ta mai da kofa ta rufe. "Areefa!!". Taji ya ambaci sunanta cikin wata murya wacce ta tabbatar bata sa bane gabadaya sautin ta ya cika mata kunnuwa yake yi kamar gidan ma rawa yake yi gabadaya lokaci guda ta sake rikicewa sosai. Kara kankame jikinta tayi sosai idanuwanta a runtse ba abinda take ambata sai sunayen Allah hawaye sai faman sauka suke a kuncita zuciyarta na kara rikicewa. A kunnuwanta take jin taku wanda yake ansawa a dukkanin bangwayen gidan ko ta ina kasa da sama zubewa tayi ta zauna kasa cikin yanayi na yanke tsammani abin da yake kokarin faruwa da ita. Bata san mai ya kai ta yarda da auren nan ba, bata san wani tsautsayi bane yasaka ta amincewa dashi, tana cikin bala'i. wanda bata san ya za ta fidda kanta ba tsoro take kar abin yayi yawa ga duka ga mari gami da tsinka jaka. Wasu hawaye masu zafi suka zubo mata daidai lokacin da taji takun kafafuwansa na takowa zuwa toilet din fargabarta ta dadu da sauri ta shiga ja da baya domin kafafuwanta take jin suna kokarin kasa daukarta handle din kofar da aka rike hakan ne ya sanyata dauke numfashi gabadaya na dan lokaci kafun ta ji an saki a juya kuma an fara tafiya a hankali jin shirun da tayi na ɗan lokaci ya sanyata sakin gwauron numfashi tana dafe kanta da yake faman sarawa kamar zai rabe gida biyu numfashi take fizga zuciyarta na kara rikicewa da wannan lamarin wanda bata san yarda zata kwatantashi ba. Haka ta cigaba da zama cikin wannan talatin daren har zuwa wani lokaci wanda ita akaran kanta ba zata iya cewa wani lokaci ta dauka ba domin barci a lokacin bata san ina ya nufa ba idanuwanta sun kekeshe kiran sallar assalatu ne ya fargar da ita daga duniyar tunanin da ta lulaka cikin kasalallan yanayi ta mike tana jan kafafuwanta da take jin su kamar zata zubda ita kasa ta isa wajan famfon Toilet bayan ta yi tsarki ta daura alwala zuciyarta na ta nazarin ta yarda zata fice daga dakin don gabadaya ta gama firgicewa bata san abin da zai faru ba in ta fita daga toilet din nan bata so ta hadu dashi ta tsane shi sosai take jin tsanarsa na kara samun gurbi a zuciyarta sosai take ganin wautar kanta da ta yarda har ta amince akayi wannan auren gashi yanzu tana cizon yatsa. Sai da ta gama tsalle tsalle da zuciyarta kafun ta tunkari kofar jikinta na faman bari ta buɗe kadan ta leka ganin ba kowa a hankali ta shiga takawa ta fito ganin tabbacin ba kowa ta karasa kusa da kofar ta mai da ta kulle gami da sargafa key wani irin numfashi ta ja gami da jingina da kofar ta runtse idanuwanta zuwa wani lokaci kafun ta buɗe ta ja kafafuwanta sallaya ta dauko ta shimfiɗa gami da saka hijab ta shiga bada nafilfili zuwa wani lokaci tana kai kukanta wajan Allah ya rabata da wannan mugun mutumin ya tsare mata rayuwa ya kare ta sosai take zubda hawaye zuciyarta na kara karaya da tashin hankalin rayuwar da take ciki a yanzu faragaba take bata san abin da zai faru ba tana tsoron abun da zai faru ya hada har da ita shiyasa tun farko ta so Maama ta fada mata komai da zai faru da ita a wannan gidan domin ta shirya amma bata yi haka ba ga shi yanzu tana ganin bala'i.... Ringing din wayar tace ya katse mata dogon tunanin da ta zauna tana ta faman yi bayan ta sallame da gudu ta mike don har ta tsoro amma jin wayarta ne ya hakan ya sanyata shiga dubanta in da ta cillar da ita jiya can ta jiyo sautin bayan loka din gadon ta da hanzari ta isa ta rarumo ta ganin Maama ne ya hakan ya sanyata sauri daga kiran muryarta na rawa. "Maama kin taho ne kina ina yanzu?". Ta fadi da ɓarin jiki numfashi Hajiya Layla ta ajje jin muryar Areefa alamu ya nuna ba abin da ya same ta. "Areefa dafatan dai kina lafiya ba abin da same ki?". "Ni dai kawai ki taho Maama don Allah ki zo ki fiddo ni daga cikin gidan nan...". Da sauri Hajiya Layla ta tare ta. "Ba maganar zuwana Areefa in har na zo Dr.Erena zai gane ke wacece kuma zai gane ni kin ga kuwa in ya san waye ke ai da matsala...". "A,a Maama ni ba damuwa ta ba ce ya san ko ni wacece in har zan fice daga cikin gidan ba zan iya zama ba ki zo ki cece ni". Ta karashe muryarta na kara karyewa da kuka sosai durkushewa tayi a wajan jin Hajiya Layla ta ce ba za ta zo ba kenan duk abin da zai faru da ita sai dai ya faru kenan. "Areefa". Hajiya Layla ta fadi amma Areefa bata ansa ta ba sake kiranta tayi nan ma bata ansa ta ba sai ma kashe wayar da tayi ta cillar da ita kan gado zuciyarta ta shiga hasaso mata wani lamari mai girma wanda take kokwanto akan sa tsakaninta da Hajiya Layla tana SHAKKA akan kalaman da take furta mata tana shakka anya ba yaudararta tayi ba domin wani kudiri nata anya kuwa ba GADAR ZARE ta saƙa mata ba ta rufta ciki. Girgiza kai ta shiga yi kamar wata kadangaruwa cikin tsayin lokaci kafun ta mike tana kai kawo cikin falon da matsanancin tashin hankali mai girman gaske sosai take jin zuciyarta na son gasgata abin da take sanar da ita sosai take jin girman lamarin a ko ina na sashin jikinta. Bata son hasashenta ya tabbata bata son maganar zuciyarta ya zama gaskiya tana tsoro akan abin da zai je ya dawo in har hasashenta ya tabbata to tabbas da matsala wanda bata san ya zata fuske ce ta ba. Zame jikinta tayi ta zauna bakin gadon hadi da zabga tagumi zuciyarta da kwanyarta sai faman hayaniya suke yi suna kokarin kamawa da wuta domin gabadaya ji takeyi komai ya rikice mata ta kasa samun tunanin da zata yi. Ihu taji gami da tsayuwar mota a lokaci guda bata san lokacin da ta zabura ba tana kokarin kwasa da gudu tayi hanyar bayi taja tunga ta tsaya tana faman rarraba idanu bata san gari yayi haske haka ba daga kai tayi daidai inda agogon dakin yake karfe bakwai har da minti hamsin 7:50 mamaki hakan tayi domin bata san lokacin ya ja haka ba nan tsaye take tana jiyo sautin ihun nata shi yana kusantowa cikin gidan sosai daidai lokacin da ka buɗe kofar falon aka shigo ta tsinkayo faduwar abu mai karar gaske har sai da ta sanya hannu ta toshe kunnuwanta gami da runtse idanunta... *_KAMALA MINNA_*😘 [10/16, 10:12 AM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU BALA'I NA. KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA HAMSIN DA HUDU Cikin hanzari ta fito daga cikin Toilet din jikinta daure da ta shawul kallo daya zaka yi mata ka hango tsantsan tashin hankalin da take ciki idanuwanta sun kaɗa sun yi jajir kamar wacce tayi KUKAN DOLE kai kawo kawai take yi gabadaya kanta ya gama kullewa ta rasa me ya kamata tayi a yanzu wanda ya dace a daidai wannan lokaci amma ta rasa gaɓadaya gaboɓin jikinta ji take yi kamar an lakaɗa mata duka ta ko ina. Da hanzari ta isa bakin gadon dakin nata ta zauna tana mai da numfashi kamar wacce tayi gudun fanfalaki wayarta da ke yashe gefe guda ta janyo tana mai dubanta tana jujjuyawa har na tsayin dakiku kafun ta shiga latsata tana binciko lamba ta danna mata kira amma ina! Wayar akashe taji ta hakan ba karamin kara rikita mata kai yayi ba mikewa tayi da sauri ta nufi sif din dake dakin buɗewa tayi ta janyo doguwa riga baƙa ta zurawa jikinta gami da yin rolling da mayafin ta janyo flatshoes ta sanya key din motarta da ke kan Mirrow ta dauka tare da dauko wayarta sai da ta karewa dakin kallo kafun ta fice cikin hanzari zuciyarta na kara tsinkewa da tashin hankali mai girman gaske. Cikin hanzari ta fice zuwa tsakar gidan motarta kirar 406 mai launi ruwan toka ta shiga tare da yi mata key bayan ta buɗe get din gidan ta fice ziciyarta na kara rikicewa ba abin da take jiyowa sai sautin muryar Areefa da yarda take kuka tana ihu akan ta zo ta taimake ta zata mutu bata san mai za tayi mata ba ba ta san abin da ya kamata tayi a daidai wannan lokacin ba tana tsoron Dr.Erena ya sake maimaita abin da ya zama shine sanadi a yanzu tana tsoron a sake komawa gidan jiya za tafi kowa bakinciki zata fi kowa takaici a duniyar nan domin komai ya faru da Areefa a yanzu da lokacin baya duk ita ce sila ta hanyarta komai ya ke tabbata. Wasu hawaye ne ta ji sun sauko mata da sauri ta sanya hannu daya tana dauke su tana mai tuki jikinta a sanyaye zuciyarta ne ta shiga kai kawo tana so ta samo wanda zai taimaka mata da abin yi sosai kwanyarta take hayaki tana kokarin kamawa da wuta. 'Alhaji Abdulwahaab' Sunan da ya zo mata kai kenan da sauri ta runtse idanunta kafun ta buɗe su tana jin wani irin yanayi a zuciyarta mai girma gaske da sauri ta gangara bakin titi tayi parking tana mai hada kanta da sitiyarin motar na dakiku sai faman sauke numfashi take kafun ta dago ta dubi wayarta lambarsa ta binciko jikinta har rawa yake yi ta danna masa kira gami da karawa a kunne cikin kankanin lokaci ta shiga ruri amma ba a daga ba har ta katse sai da tayi haka sau uku a na hudu Allah ya taimaka ya dauka wani irin ajiyar numfashi tayi mai karfi tana mai cewa. "Don Allah kana ina Alhaji Abdulwahaab akwai matsala fa sosai ina bukatar ka yanzu yanzun nan ko ina kake ina kan hanyar gidan Dr.Erena mu hadu acan". Mamaki sosai ya cika shi jin abin da take fadi. "Ban fahimce ki ba Hajiya Layla meke faruwa ne?". Dafe kai tayi kafun ta sake nisawa. "Ba mu da lokaci don Allah ka zo yanzun nan akwai matsala ce". numfashi ya sauke cikin wani yanayi. "Amma Hajiya Layla kin mata yanayin da muke ciki ne da Dr.Erena kin san za a samu matsala in har ya gane mu din ne muke tare da Areefa...". "Alhaji Abdulwahaab!". Hajiya Layla ta kira shi tana mai katse shi zuciyarta na kara hargitsewa. "wannan lokacin ya dade da shafewa na manta dashi yarinyata nake bukata Abdulwahaab duk wani boye-boye ya kare tsakani na dashi zan fuskace shi komai zai faru zan tunkare shi sai dai duk abin da zai faru ya faru". "Hajiya Layla da kin yi hakuri man...". Katse wayar tayi jin yana kokarin bata mata lokaci wani kuncin taji ya tokare mata wuya mai Alhaji Abdulwahaab yake nufi da nuna halin ko in kula akan wannan lamarin da ta sanar dashi anya kuwa ya san abin da yake yi anya kuwa ya ji abinda ta fada masa sosai dafe kai tayi na dan lokaci kafun tayi wa motar ki ta fizge ta da karfi zuciyarta cike da zullumi. Tafiya sosai tayi sannan ta isa unguwar da Dr.Erena yake nesa da gidan tayi parking zuciyarta ta na bugawa da sauri sauri bata san mai zata yi ba sosai take fargaba da tsoro a zuciyarta Areefa take so ta gani so take yi ta ga halin da take ciki runtse idanu tayi gami da kashe motar ta fito ta mai da kofar ta rufe a hankali ta shiga takawa zuciyarta na kara sautin bugu har ta isa bakin get din gidan lekawa ta shiga yi ko zata hango cikin gidan amma ba ta hango komai ba gefe ta ja kadan tana duban layin amma ba kowa sit kake ji kamar mutuwa ce ta gifta hakan ya dan kara tsorata ta amma cikin karfin hali da nuna rashin tsoro ta shiga kwankwasa Get a hankali idanuwanta na saitin karamar kofar zuciyarta na kara sautin bugun ta. "Waye a nan?". Ta ji an fadi da sauri ta juya don jin muryar tayi kamar daga sama domin gabadaya a firgice take sai da ta saita kanta sannan ta lura ashe Maigadi ne wanda ya buɗe kofar a daidai wannan lokacin. Yak'e ta shiga yi shikuwa sai faman gaisuwa yake watsa mata ganin Babbar mace ce mai suffar naira. "Yawwa Alhaji na ciki kuwa?". Ta fadi tana mai kokarin saita kanta sai da ya kare mata kallo don ya so gane rikicin da ke idanunta kafun ya gyaɗa kai alamun eh wani rugugin tashin hankali ne ya dirar mata a zuciya amma ta danne tana mai kara faɗaɗa yak'enta kafun ta numfasa. "Ok ni mahaifiyar matarsa ce Areefa". Da sauri ya kara ladab yana mai bude mata kofar domin ta shiga sai da tayi addu'a kafun ta saka kafafuwanta cikin gidan tana takawa tana bin ko wani sashi da lungu na gidan tana kara tsorata da Dr.Erena irin dukiyar da ta ga an zuba a gidan ta fitar hankali ba ta lura da motar dake gabanta ba har ta kusan cin karo da ita san nan tayi baya da sauri motar tabi da kallo ganin yanayin da take da sauri ta zaro idanu waje ganin yarda motar tayi gilashin fitilun duk sun fashe mamaki ne ya cika ta da tsoro a zuciyarta tana tambayar mai ke faruwa Allah yasa ba Areefa ba ce tayi accident wani irin bugawa taji gabanta yayi da sauri ta yi cikin falon tana zuwa ta tadda shi a bude ba tare da fargabar komai ba ta fada ciki baje ta hango mutum tsakiyar falon sai faman murkususu yake yi idanuwansa a kankafe da sauri ta ja baya tana mai kiran Areefa da karfi gidan gabadaya ya dauka sautin muryarta. Hancinta ta toshe jin irin warin dake tashi a tsakar falon gabadaya taji zuciyarta tana sama da kasa kamar zata yo waje rarraba idanu ta shiga yi tana faman kiran Areefa ganin ba alamunta hakan ya sanyata nufar cikin falon sosai tana buɗe daku har ta haye saman benan dakunan da ta gani ajere guda uku ta nufa tana kiran Areefa kamar wacce makoshinta zai yo waje. Ita kuwa Areefa da take can kulle cikin daki kamar daga sama ta tsinkayo Muryar Hajiya Layla bata gasgata ba ta dauka kawai halin firgicin da take ciki ne take jiyo sautin kamar na ta amma kuma sai taji sautin na daduwa da sauri ta mike ta buɗe Toilet din kamar daga sama ta ji ana kwankwasa kofar dakin da take muryar Hajiya Layla na tashi da gudu ta fito har tana tuntuɓe ta nufi kofar ta buɗe da sauri Hajiya Layla ta gani a tsaye da sauri ta isa gareta ta rungume ta tana faman sakin ajiyar zuciya mai karfi idanuwanta sai zubda hawaye suke. "Areefa me ke faruwa ne haka?". Dago kanta tayi daga kafaɗarta ta dube da jajayen idanuwanta. "Maama Dr.Erena zai kashe ni ba zan iya zaman gidan nan ba wallahi na hakura ba zan iya zaman aure dashi ba don Allah ki fidda ni daga cikin gidan nan ji nake kamar numfashi zai katse". Dubanta take yi sosai ta na hango rashin hayyaci a idanuwanta gami da firgice janta tayi cikin dakin gami da mai da kofar ta rufe bakin gado suka zauna Hajiya Layla tana dubanta kafun ta nisa lura da tayi ba abin da ya same ta. "Amma me ke faruwa dake haka duk na ganki a wannan matakin AREEFA?". Runtse idanu tayi hawaye suka zubo. "Maama baki jin warin da nake ji ne?". Ta fadi muryarta da rauni a ciki tana faman girgiza kai. "Tun ranar da na zo gidan nan nake jin wannan warin har izuwa yau kuma wallahi daga jikinsa ne warin nan ke fitowa da farko nayi zaton wani mushe ne a cikin gidan amma ban gani ba sai jiya da muka hadu dashi a falo nake jin warin na fitowa daga jikinsa zuciya ta dinga tashi". Kure ta tayi da idanu kafun ta saki murmushi wanda ya jefa Areefa a wani mataki na mamaki. "Mai ya same shi na ganshi baje a falo yana faman murkususu". Zaro idanu Areefa tayi gami da mikewa. "Wallahi ban sani ba ni dai dazu naji faduwar abu gami da ihu to a tsora ce nake ban fita ba". Mikewa tayi ita ma ta ja hannunta suƙa fito ganin sun nufi falon hakan ya sanya Areefa turjewa tana duban Hajiya Layla. "Maama..". Daga mata hannu tayi gami da nuna mata alamun tayi shiru ba ta sake magana ba ta bi bayanta gabanta na bugawa ga warin da take ji yana karuwa sosai hannu ta saka ta rufe hancinta har suka isa falon zaune suka hango shi ya jingina da kujera sai gumi yake yi kamar wanda aka watsa wa ruwa hannayensa duk biyun dafe da kai sakin Areefa tayi ta isa gareshi tana mai yi masa wani irin matsayacin kallo kafun ta saki wani murmushi wanda shi kuma a daidai lokacin ya dago kansa ya sauke a saitin ta. Kallo yake binta dashi na alamun na sanki sosai yake maimaita kallon nasa akanta zuciyarsa da kwanyarsa suna kwaso masa abubuwa da suka shuɗe na shekaru masu yawa runtse idanu yayi ya buɗe su bakin sa ya shiga motsawa a hankali yana mai runtse idanuwansa shi kadai ya san wahalar da yake ciki. "Hajiya Lay...". "A kul! din ka karka sake kar ka so ma ambatar sunana da wannan bakin naka". Ta nuna shi da yatsa kafun cigaba da fadin. "Ashe ka gane ni ai na dauka ka mance fuskata a duniyar rayuwarka". Sosai yake cikin tu'aji da daurewar kai tashi yayi sosai daga jikin kujerar ya juya ya dubi inda Areefa take tsaye kallon ta yayi kafun ya juyo ya dubi Hajiya Layla. "Me ya kawo ki gidaɓaa me kika zo yi ba na ce miki karki sake na sake haduwa da ko mai kamar ki bane". Ya fadi yana mai cizon labbansa idanuwansa na kara kaɗawa sosai kwaɓe baki tayi kafin ta nuna shi da yatsa. "Dr.Erena kenan kana tunanin zan bar rayuwarka ne ai duk wanda ya dama dani to wallahi tare zamu shanye na san zakayi mamakin ganina a gidan ka ko?". Ta fadi tana mai murmusawa. Mamaki ne ya sake cika shi tare da firgice mai girma domin shi dai ya mance da wata Hajiya Layla a duniyarsa tun da kuwa ya ganta a yanzu akwai wani abu tattare da ita. "Dr.Erena Attajirar duniya". Ta fadi tana barkewa da dariya wanda sosai ta kaɗa cikinsa amma ya ki nunawa ya shiga kokarin tashi amma ya kasa rikewa yaji bayansa yayi ji yake yi kamar ana doka masa guduma. "kar fa ka damu kan ka ba wani abu bane Malam Nata'ala ne ya bani sako in ba ka ai na san ba zaka mance sunan ba ko?". Ta fadi cikin yanayi na izgilanci. 'Malam Nata'ala'. Can kasar makoshi yana tunanin inda ya san sunan kwanyarsa ne ta fara shawagi da sunan amma har ta gama bai canko ba illa idanu da ya zubawa Hajiya Layla da take ta faman sakin murmushi. "nayi mamaki da naga komai naka ya fara sauyawa wai yau kai ne da yin aure da alamun dai komai dake faruwa kwanyarka bata daukar sa da alamun kuma tarihi zai maimaita kan sa". Duban Areefa tayi kafun ta dubi Dr.Erena da yaje ta faman cizon laɓbansa kamar zai cizge su daga jikinsa. "wannan ita ce matar taka?". Ta fadi cikin yanayi na rainin hankali a hankali ta taka ta isa wajan da Areefa take tsaye ta dafa mata kafaɗa kafun ta sake ta dawo ta zauna cikin daya daga kujerun falon tana dora kafa daya kan daya gami da duban Dr.Erena da kan sa ya shiga wani mataki na rashin aiki komai yake ji yana cinkoshe masa ya kasa tuna komai a daidai wannan lokacin. *Afuwan naji na shiru kwana biyu kusan yanayin garin sai a slow yau fari gobe baki haka rayuwar take dafatan ba kuyi fushi ba😎😎 ina tare da ku ina irin mugin kaunarku din nan*👏👏👏 *Kamala Minna*😘😘 .UKU BALA'I NA. KAMAL MUHAMMAD LAWAL. (KAMALA MINNA.) 07039355645 *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร BABI NA HAMSIN DA BIYAR Dubanta yake yi cikin wahalallan yanayi zuciyarsa na ta faman kokarin bankado masa abin dake boye amma kwanyarsa sai hayaki take yi masa ji yake yi kamar ya mike ya shaƙo Hajiya Layla don ya tabbata akwai wani boyayyan al'amari game da ita zai iya cewa ma halin da yake ciki a halin yanzu ita ce sanadi ba kowa ba runtse idanunsa yayi gami da sakin wani nishi mai karfi kamar macen da ke nakuɗa. "Hajiya Layla mai ya dawo dake rayuwata a daidai wannan lokacin kuma meye hadinki da MATATA?". Ya fadi cikin yanayi na azaba da raɗaɗi da yake jin ko ina na jikinsa ya dauka numfashin sa sai sama da kasa yake yi. "Dr.Erena kenan kana tunanin akwai abin da zai sake dawo dani rayuwarka a wannan karnin kar kayi zaton wani abu amma abu daya nake so ka tuna a rayuwarka shi ne Sharri dan aike ne duk in da aka tura shi zai je ya dawo abu daya nake so ka kuma tunawa shine Malam Nata'ala". Areefa da ke tsaye tun dazu idanuwanta na tsiyayar da hawaye Hajiya Layla ta dube ta sosai kafun tace da ita. "Zo ki samu waje ki zauna mana kin tsaya a tsaye in har kika ce kallon wannan mutumin za ki din ga yi kina zubda hawaye kina da aiki sosai a gabanki hawaye ya kamata ace ya tsaya miki a wannan matakin da kike". Girgiza kai tayi tana mai sake watsawa Dr.Erena wani matsiyacin kallo ji take yi kamar ta shako shi ta kashe shi don wata tsanarsa take jin na sake buɗe fili a zuciyarta mai girman gaske. A hankali ta shiga takowa tana isowa gareshi warin da take ji yana tashi daga jikinsa shi yafi komai tayar mata da hankali idanunta ta runtse gami da rike numfashinta idanuwanta akafe akan sa ba abin da ke cikin su sai zazzafar kiyayya mai girman gaske shi kansa sai da yayi mamaki kan irin kallon da take masa kau da kai yayi yana tambayar kan sa mai ke shirin faruwa dashi ne tun da ya tashi yau ya rasa gane kansa tun kafin ya isa wajan aiki ya samu tsautsayin haduwa da yan fashi ko makasa zai ce masu oho suka yi masa dukan shan gishiri gami da kwace jakar makuɗan kudaɗen da zai je da su Company din sa domin zubawa ga wata harkalla da akayi masa tallarta ya amince zai yi ta. Bayan sun dake shi sun fasa masa mota sun kwace kudaɗen kuma wanda hakan bai dame shi ba akan yarda yake jin jikin sa a yanzu sosai ya fara fargabar abin da yake kokarin faruwa dashi a yau din fuskar Hajiya Layla da ta bayya a gareshi akanta ya diga ayar tambaya. Kofar da aka turo aka shigo ne ya sanya shi tsinke zaren tunanin sa sosai yake bin kofar da kallo a daidai lokacin yayi arba da Alhaji Abdulwahaab suna kallon junansu ido cikin ido mamaki al'ajabi ya sake narkar dashi kau da kai yayi tare da runtse idanuwa yana mai tambayar kansa mai ya kawo Alhaji Abdulwahaab gidan sa a daidai wannan lokacin ganin abin yake yi kamar a mafarki ba gaskiya ba sai faman jan numfashi yake wanda yaji yana kokarin kwace masa. A hankali ya shiga takowa tsakiyar falon yana dubansu su duka cikin wani irin yanayi musamman yarda ya ga Dr.Erena aciki abin ya bashi mamaki gefe ya koma ya tsaya yana duban Hajiya Layla da ita ma shi take duba. "Ka zauna mana". Ta fadi tana nuna masa kujera, gyaɗa kai yayi tare da zama bakin sa cike da tambayoyi masu yawan gaske amma ya rasa ta ina zai fara ko da yake akwai abin da yake hasashe akan faruwan haka... Muryar Hajiya Layla ce ta katse masa tunanin da yake yi. "Lokaci yayi sakon Malam Nata'ala zan isar kamar yarda ya bani shi amma bisa mamaki shi ya manta da waye ma Malam Nata'alar". Ta karashe tana sakin wani mugun murmushi kafin ta mike kan kafafuwanta da hanzari ta shiga kai kawo a tsakar falon hannayenta goye a bayanta. **** A hankali take jan motar cikin yanayi na fargaba da tsoron yanayin wajan haka kawai take jin zuciyarta na gargaɗin ta akan ta koma kar taje amma wani sashin na kara mata kwarin gwuiwar zuwa din runtse idanu tayi tana kara kurɗawa cikin dajin da tun da take a filin duniyar nan bata taba zaton akwai wannan dajin ba. Tafiya tayi sosai har ta fara yanke tsammani da rabon samun abin da ta zo nema ji take yi kamar kwatancen da Areefa tayi mata ba haka bane domin ta fara sarewa da tafiyar nan da ta kwasa kamar wacce zata bar duniya. Burki ta taka da sauri ganin uban tafiyar taki karewa gashi wani abun da take shirin gani ta baro surkukin daji amma nan kuma ta fara hango filin Allah kamar an share shi hakan ya fadar mata da gaba ba tare da ta karasa shiga filin ba don zuciyarta sosai ta tsoratar da ita akan ko wani mugun abun ne a shimfiɗe a wajan. Shiru tayi tana tunano labarin da Areefa ta bata akan zuwan su gidan Malam Nata'ala sosai ta fara gano komai da sauri ta sakeyi wa motar key ta fizgeta bayan ta nemi tsari wajan Allah da ya kareta daga duk wani abun ƙi da yake tattare da wannan wajan ba ta gama wannan tunanin ba ta fara hango wani farin gida daga can tsakiyar filin wanda ya kasance shi kadai hakan ya tabbatar mata gidan kenan. Tsayar da motar tayi gami da kasheta baki daya ta shiga kallon gidan yana yarda Areefa ta kwantata mata ba abin da ya sauya daga cikin sa mamaki ne ya cika ta dama a duniyar nan a irin wannan dajin har za a samu wanda zai iya rayuwa a cikinsa shi kadai ba tare da wani ba girgiza kai tayi gami da buɗe murfin motar ta fito a hankali ta fara takawa cikin yanayi na tsoro bayan ta rufe motar tana tafiya tana waiwaye don gabadaya tsigar jikinta ji take yi tana tashi kanta yayi mata nauyi sosai. Gidan taga kamar yana sauyawa a idanuwanta tsoro na kara shigarta amma duk da hakan bata daina kusantar gidan ba a haka har ta isa kofar gidan a buɗe yake hakan ya bata damar shiga ba tare da wata fargaba ko tsoron da take ji zuciyarta na kawo mata ba lokaci guda taji duk wata fargaɓar na raguwa sosai. A tsakar gidan ta tsaya tana mai kallon cikinsa komai tsaf-tsaf kamar gidan sabuwar amarya. Daki guda ta hango wanda labule ke sake wajan ta nufa tun da ta tunkari wajan take jin wani wari na kawo wa hancinta farmaki da sauri ta buɗe jakartaa ta zaro farin hankicif ta toshe hancinta amma duk da hakan ba ta daina jin warin ba. Hannunta daya ta saka ta buɗe labulan da sauri ta saki gami da ja da baya idanuwan ta a warwaje abin da ta gani yayi matukar faɗar mata da gaba nan ta shiga ambaton Allah da neman tsari sai da ta kwashe mintina kafun tayi kundunbalar sake buɗewa hango shi tayi kan buzu a takure sai ka rantse ba mutum bane a wajan fuskar nan tayi kaca-kaca da kasumba zallar fuskar tashi ba ka gane wa kafarsa kuwa guda daya sai faman wari take yi kana hango tsutsuni na yawo a cikinta. Runtse idanu tayi lokaci guda taji wani tashin hankali ya ziyarce ta zuciyarta ta karye hawaye ya shiga zubo mata lokaci guda a hankali ta jingina da bango tana jin yarda kanta ke juyawa kamar zata zube a kasa numfashinta na sama da kasa. "Baiwar Allah". Kamar daga sama ta tsinkayo muryarsa wanda hakan yayi matukar bata mamaki jin muryarsa raɗau kamar ba wanda yake cikin mawuyacin hali ba dubansa ta shiga yi da buɗaɗɗun idanuwanta zuciyarta na tsalle da tsoro. "Me ya shigo dake wajan nan kin san bala'in da ke cikin nan kuwa kinsan masifar dake tattare da wannan wajan kuwa kiyi wa kanki fada in ma wani abu ki ka zo nema to kiyi maza ki fice tun kafin wani abu ya same ki". Kalamansa taji suna yi mata yawo a kwanya da sauri ta durkushe tana dubansa kafun daga bisa tayi kokarin yi masa sannu bai ansa ta ba illa kau da kai da yayi wani hayaki ne ta ga yana fitowa daga bangon dakin na hagu yana shawagi a tsakar dakin yana murɗewa hakan ba karamin kara rikita Hajiya Layla yayi ba da sauri ta fara ja da baya tana kokarin ficewa daga dakin. "Na san abin da ke tafe dake kuma nayi murna sosai da kiƙa zo a daidai wannan lokacin Dr.Erena ko na san akan sa kiƙa zo nan ba zan boye miki ba na san na cuce Khairiyya a rayuwarta nayi dana sani domin tun daga kanta na fara fuskartar matsalolin rayuwa har zuwa wannan lokaci da nake wannan halin...". Tari ne ya sarke shi wasu abubuwa su ka shiga zubowa daga bakin sa kamar tsutsotsi sai motsi suke yi Hajiya Layla gabadaya ta rikice ji tayi fitsar na kokarin kwace mata. "Ki tashi ki tafi lokaci na nan zuwa kuma Dr.Erena shima sai ya dandani bala'in da nake ciki banta taba mugun aiki ba kamar yarda nake yi wa Dr.Erena shine mutumin da naƙe yi wa aiki wanda ni akaran kaina ina tsoro da fargaba in ina yin sa sannan ina kara jinjina rashin imani irin na Dr.Erena domin kuwa a duk sahun mutanan da nake yi wa aiki shine yafi kowa kawo mani mugun aiki". Shiru yayi yana jan numfashi kafun ya sake fadin. "yace zai yi aure ko kuma tsarin aikin da nayi masa babu zancen aure har gaban abada to wannan auren shi zai zama SILAR AJALI gareshi duk ranar da aka daura auren to tabbas shima yarda na zama shima haka zai zama yarinya ta shi ki tafi tun kafin wani abu ya same ki sannan karki sake ki hana Khairiyya aurensa ki bari a yi ko da na rana daya ne na tabbata daga wannan ranar salo zai sauya". Mamaki ne ya cika ta zuciyarta na kara karyewa da tashin hankali mamaki take yi sosai da maganganun Malam Nata'ala tun da take a rayuwarta yau ne rana ta farko da ta ji ta tsani duniyar nan gabadaya taji ta tsani zama cikin ta... "Da hannu na nake amfani da ayar Allah tsarkakankiya domin biya masa bukata ina amfani da jinnu a nan Dr.Erena ya sha cin naman jarirai wanda aka dafa su da ayar Allah da wani suddabaru na jinnu ya sha zuwa da mace mai dauke da ciki wanda bai haura wata biyar ba in saka jinnu su barar dashi tare da yi masa magani don kawai yana so ya zama daya daga cikin ATTAJIRAN DUNIYA nayi da nasani nayi kaico da rayuwata da ta kasance a haka na san ko a lahira bani da wani amfani hukunci na mai girma ne domin tawa ta kare amma ki sani yarda na shiga bala'i shima sai ya shiga nan kusa kadan Sharri dan sako ne ya na nan tafe gareshi". Yana gaman fadin haka nan ya shiga tari wannan abubuwan masu kama da tsutsotsi na sake zubowa kamar an buɗe wani matattarar su tana kallo wannan hayakin ya shiga wuce ta cikin hancin sa jikinsa lokaci guda ya shiga canzawa yana baƙi gami da ruwan toka kansa da duk wani gashi dake jinsa yana canzawa zuwa fari gami da fidda wani hayaki da sauri ta rarrafa ta fice daga daki gabadaya ta gama rikicewa ta fice daga hayyacin ta tashin hankalinta ya kara ninkuwa duniyar gabadaya tana tsoron ta cikin yanayi na ɓarin jiki da rashin hayyaci ta fice daga gidan idanuwanta a rufe kawai jefa kafafuwanta take yi har Allah ya kaita inda motarta take.. **** Hawaye ne ke zuba sosai a idanuwanta zuciyarta na kara karyewa bata so tuna wannan labarin ba amma ba yarda zata yi domin ta gama tsorata da halin da ta tsinci Malam Nata'ala a ciki wani tsoron Allah take ji yana samun gurbi a zuciyarta duniyar take ji gabadaya ta fice mata daga rai duban sa tayi kafun ta dauke hawayen da suke zuba mata. "nasan yanzu zaka tuna labarin da ya shuɗe sama da shekaru ashirin da doriya a duniyar ka na san zaka tuna yarinyar da ka lalata mata rayuwa yarinyar da kayi amfani da ita don kawai cikar burin ka Khairiyya da kasani to ita ce wannan Areefa da ka aura da sunan matar aure na san kuma zaka tuna waye Malam Nata'ala". Kuka ne ya ci karfin ta da sauri ta toshe bakinta da hannayenta tana duban Areefa wacce gabadaya kukan take yi da shassheka kamar numfashin ta zai dauke. Wani irin tari ne suka ji ya sarke dashi hannunsa daya a saitin Areefa idanuwansa lokaci guda suka shiga sauyawa fizga yaji numfashin sa nayi kamar ransa zai fita gabadaya ya gama rikicewa da labarin da yaji domin ya manta da wani mutum wai shi Malam Nata'ala.. *Kamala Minna*😍😍 Gaskiya Shafin nan fa ya burgeni Ko ya kuka ce makaranta kuma.kuce wani abu🤷‍♂🤷‍♂🤷‍♂🤷‍♂😆😆😆😆 [10/17, 9:39 AM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU BALA'I NA. KAMALA MINNA. *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA HAMSIN DA SHIDA. Tsaye yake jikin motarsa ya harɗe hannayensa saman kirji idanuwansa sunyi mici-mici alamun bacin rai duban ta yayi a karo na ba adadi ya na jan tsaki kamar harshensa zai tsinke. "Baki da hankali Hafsat na lura kan ki rawa yake yi dakikanci da jahilci su ne suke karanta miki karatun hauka kika zo kina sauke mani to ba zan dauka ba don na rantse da Allah na fiki tashanci duk akuyancin ki". Ya fadi yana mai kara tsuke fuska Hafsat dake tsaye sai faman jinjiga take yi kamar wacce ake kaɗawa gangi duban sa tayi sosai cikin takaici da rashin abin yi. "Huzaif haka ma zaka ce dani ga mari ga tsinka jaka to wallahi ba ka isa ba kayi kadan an gaya maka zan dauki rainin wayon ka ne duk wani ihukan banza da zakayi mani wallahi ba za suyi tasiri akai na ba". Tun daga kasa ya fara kallon ta yana yatsine fuska kamar wanda ya ga sabon kashi sai da yayi mata kallon tsaf! Sannan ya tsartar da yawu ya juya yana kokarin buɗe motarsa ya shi gami da fadin. "In da na san wannan haukar zakiyi mani da kika kira ni wallahi ba abin da zai kawo ke na rantse da Allah da ga yau zamu raba jaha don ba zaki dauko kamayamaya ki jona min ba ina zaune kalau ki jaza min salalar tsiya an gaya miki ban san halin da kike ciki bane ban san abin da kike yi bane wato gani karkatacciyar kuka mai dadin hawa ko to kin yi kadan Huzaif daban yake ba irin mazajen da za ki wanke tas! bane". Ganin da tayi yana kokarin faɗawa cikin motarsa da sauri ta zabura ta isa gareshi gami da rike murfin motar da ya buɗe kallon ta yayi ido cikin idanu itama kallon shi take yi kafun ta kau da kai. "Kasan Allah Huzaif yarda muka dama tare da kai wallahi sai mun shanye shi a filin duniyar nan ba wani na miji da nake hulda dashi sama da kai kaima kasan haka amma saboda tsabar ka raina mani wayo shine zaka nuna min halin-ko-in-kula gaskiya da sake". Kallon ta yake yi sosai cikin tsana da takaici wai har wannan kucakar yarinyar ce za ta dubi tsabar idanunsa tana masa rashin kunya shi kam! bai san tsautsayin da ya hadashi da wannan mahaukaciyar yarinyar ba har sukayi tarayya bai san ina tunaninsa ya shiga ba bai san ina hankalinsa da lissafin sa suka fada ba har hakan ta faru a gareshi. Daga hannu yayi kamar zai kwaɗa mata mari da sauri ta ja da baya tana mazurai hakan da ya gani ya bashi daman faɗawa cikin motar da sauri yana kokarin rufewa ita kuma tayi hanzarin riko murfin saura kadan ya datse mata hannu kallonsa take idanuwanta sun kada sunyi jajir kwalla sai surnano mata suke yi kau da kai tayi cikin raunanniyar murya. "Huzaif bai kamata kayi mani haka ba kai kan ka ka sani ba ni da wani wanda muke hulda dashi sai kai amma na ga kana kokarin baɗa min kasa a ido kana kokarin bari na da masifa da bala'i ya kamata kayi tunani mana...". Wata tsawa ya daka mata gami da zaro idanuwansa waje da sauri ta saki murfin motar ta ja baya fitowa yayi gabadaya yana nuna ta da yatsa bakin sa sai rawa yake yi kamar wanda zai ci babu. "Karki sake karki soma don wallahi in har kikayi kokarin laƙa mani wannnan abin kin ji na rantse danginku gabadaya sai na daure su har igiya tayi rara don ba zan dauki Nosense things din nan ba". Kallon sa take yi cike da mamaki maganganunsa ne suke mata yawo a kwanya ji take yi jiri na kwasarta kamar zata watse a kasa runtse idanu tayi don ba ta gasgata wai Huzaif bane ya daka mata tsawa har yake fada mata wadannan kalamai ina ba zai taba yuwuwa bane. Buɗe idanuwanta tayi sosai akan sa tana dubansa. "Kasan Allah Huzaif baka isa ba".. Ta fadi tana takowa gareshi wuyar rigarsa ta cafka ta rike gam! ta shiga zazzaga masa rashin mutuncin tana faman firirita da girgije-girgije takaici ya kule shi bai san lokacin da ya dauketa da wani wawan mari ba wanda ya sanyata sakin kara ta runtse idanu wasu taurari ta ga su na yi mata yawo a saman kai gabadaya ji tayi duniyar na juya mata buɗe idanunta tayi hannayenta dafe da kunci kallonsa take yi da wani irin yanayin wanda bata taba zaton zata samu kanta a cikin ba wai Huzaifa ne ya mareta ina mafarki ne wannan ba gaskiya ba zata so ta farka daga wannan dogon malalacin barcin da take yi laɓɓanta ta tura cikin baki gabadaya cizawa tayi jin zafi ya sanyata tabbatar da cewa eh da gaske ne komai ke faruwa. Juyawa tayi tana duban layin nasu mutanan da suke kai kawo ta hango suna kallonsu hakan yayi matukar bata mata rai ba ta san lokacin da ita ma ta fidda hannu ta zabga masa mari ba tana faman huci kamar wata kububuwa idanuwanta sun kaɗa sun yi jajir kwallar da take makale da ita ta sake zubowa. Shikam! A bazata yaji marin hakan ba karamin rikita shi yayi don sosai ya ji marin hannu ya saka da sauri ya shafi kuncin nasa sannan ya dubi hannun nasa mamaki ya turnuke shi tare da bakin ciki da takaici yau karo na biyu kenan a duniyar nan 'YA MACE na daga hannunta ta na marin sa bai san mai ya sa ba kuma abin takaici kananan yara kamar wadannan kuma yan gida daya runtse idanu yayi zuciyarsa na shiga wani irin kunci hannunsa ya sake kai wa fuskarsa ya shafi wajan da ya ji marin kafin ya buɗe lokaci guda ya cafko wuyan ta ba tare da tayi zato ba sosai ya rike mata makoshi ta shiga kakari idanunta sukayo waje sosai dukansa tashiga yi amma ina ko a jikinsa sai ma idanunsa da ya saka cikin nata cikin tsantsar bakin ciki da jin haushi. Sai da ya ga numfashin ta na kokarin kufce mata sannan ya watsar da ita akasa ta baje tana faman rike wuyanta sai murkususu take yi da sauri ya fada cikin motarsa ya ja ya bar layin. Izuwa lokacin sosai mutanan layin sukayi cincirindo suna kallon ikon Allah ba wanda yayi kokarin zuwa ya kwace ta domin sun jima da sanin halin rashin kirki irin na Hafsat kuma akan idanunsa mafiya yawan lokaci Huzaif yake zuwa ya dauke ta ya fita da ita ba irin bakin halin da ba su sani ba da rashin mutunci da suke yi ita da Huzaif. Mariya dake tsaye tun dazu bakin kofa idanuwanta na faman tsiyayar da hawaye takaici duniya duk ya gama cika mata zuciya hawaye sai faman safa da marwa suke yi takaici take yi yarda ɗa namiji yake wulakanta mata yar'uwa a gaban idanunta girgiza kai ta shiga yi abin na ci mata rai ba ta son abin da zai sake daga mata hankali a wannan matakin wanda take ciki ma ya ishe. Ba tayi mamakin abin da Huzaif yayi ba don kadan daga aikin sa sosai take tuna kalamansa a ranar farko da suka fara haduwa sosai take tuna yaudararsa da yayi mata baza ta taba mantawa ba hannu ta sa ta shafe fuskar ta a hankali ta shiga takowa zuciyarta na kara curewa waje guda har ta iso wajan da Hafsat take durkushe tana ta faman rusar kuka dafa kafaɗar tayi. "Bai kama ta ki zauna kan layi kina kuka ba wannnan ba mutuncin ki bane sannan bai kamata ki zauna kina fada da namijin da kika san yafi karfin ki ba...". Wata irin tsawa ta daka mata gami da bige mata hannu da sauri Mariya ta ja baya tana dubanta cikin mamaki dago idanuwanta tayi wanda suka gama kaɗawa sukayi jajir ta watsa mata wani mugun kallo. "Ina ruwan ki ko gayyarki nayi tsohuwar munafuka duk ba dake aka hada baki aka kashe mani rayuwa ba kuma wallahi ki rubuta ki ajje yarda na gamu da bala'in nan ke ma ki tsumayi naki don ba zan shiga duniyar takaici ni kadai ba". Da sauri Mariya ta waro idanuwa waje tana ambatar 'Innalillahi wa inna ilair raji'un'. juyawa tayi ta dubi mutanan da sukayi cirko-cirko suna kallonsu wani takaicin ya sake kular da ita da sauri ta bar wajan idanuwanta na zubda hawaye ta fada cikin gida sai faman jan numfashi take yi kamar ranta zai fita. Umma dake zaune ta dube ta ganin yanayin da ta shigo ya sanyata mikewa ta nufi cikin dakin zube ta hangeta saman katifa sai faman numfarfashi take yi. "Lafiyar ki kuwa Mariya me ke damun ki ne haka?". Dago jajanyen idanuwanta tayi ta dubi Umma tana faman cizon laɓɓa. "Hafsat ga ta can a waje suna dambe da namiji Umma mutane sun hadu sai kallon su suke yi". Gaban Umma ne ya yanke ya fadi tana ambato innalillahi gami dafe kirji idanuwanta a waje. "Fada fa kika ce?". Kai ta daga mata gami da komawa ta kwanta zuciyarta sai nukurkusa take yi kanta na faman juya mata. Jikin Umma sosai yayi sanyi a hankali taja jiki ta koma ta zauna gefe guda gami da zabga tagumi abin duniya duk ya damu yayi mata yawa tausayin Hafsat take yi tun lokacin da ta lura da halin da take ciki duk da Goggo bata fada mata ba amma ita ta gane ai irin wannan abun ba ya buya koman daren dadewa sai ya bayya abu daya take gudu shine Abulle ta sani don sai ta fi kowa shiga tashin hankali. "Wai Umma me ke damun Hafsat ne yanayin da naji suna hayaniya da Huzaif kamar akwai abin da ya shiga tsakanin su ne wanda shi kuma bai yarda shine mai laifi ba...ko dai Hafsat...". Sai kuma tayi shiru ta kasa fadin abin da tayi niyya ganin irin kallon da Umma ta watsa mata na gargaɗi. "Ba ruwanki Mariya ki kame bakin ki ban son abin tashin hankali wanda nake ciki ma ya ishe ni kin san dai halin Goggo yanzun nan ta sauke miki laifin...".. Dago labulan da akayi ne ya sanya Umma saurin tsuke bakin ta Goggo ce ta fado dakin tana zuwa ta damki Mariya ta shiga jibga sai da tayi mata duka sosai Umma na kallo ba tare da ta ce da ita komai ba itama Mariya bata ko motsa ba. "Wato ke saboda kin dauki mugun abu irin na dangin uwarki shine zaki saka saurayi yayi wa Hafsat cin mutunci akan titi haka ko to wallahi ba ki isa ba yarda kika sanya aka ci mata mutunci to wallahi ke ma sai kin samu daidai dake...". "A,a kam Allah ba zai taba daura mata laifin da bata san dashi ba ai duk tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa kan dako". Kamar daga sama suka jiyo muryar gabadaya suka juya da sauri Abulle ce tsaye idanuwanta sun kaɗa sun yi jajir kallo daya zaka yi mata ka gane tashin hankalin da take ciki mai girman gaske duban su tayi daya bayan daya kafun ta ja wani numfashi mai zafi ta dubi Goggo. "Meye laifinta Goggo akan me zaki dake ta ai ba ita ce sanadi ba komai ya faru ita waccen maras hankalin wacce bata san darajar kanta da kimar ta ba ita zaki je ki daka saboda tsakaninku ne ku kukayi kidin ku kuma ku zakuyi rawar ku". Hawayen da take makalewa suka zubo zuciyarta take ji tana harbawa kamar zata faso kirjin ta ta fito ga wani irin nauyin da kanta yayi idanuwanta suna lumshewa a hankali taji duniyar na juya mata kokarin juya tayi domin fice wa amma ina lokaci guda kafafuwanta suka lauye suka watsar da ita akasa da hanzari umma ta isa gareta cikin tashin hankali bata san lokacin da ta fashe da kuka ba dama ta san za ayi haka. Jinjigata ta shiga yi amma ina ba alamun motsi a jikinta da sauri Mariya ta mike tayi waje da gudu ta kamfato ruwa ta kawo Umma ta watsa mata amma ina ba alamun motsawa duban Goggo tayi dake tsaye kamar wacce aka dasa sosai jikin ta yayi sanyi amma ta kasa tabuka komai. Sake sheka mata ruwanta yi sosai wani numfashi ta ja kirjinta yayi wata irin harbawa da sauri Umma ta dagota idanuwanta da suke rufe ta buɗe su kadan hawaye masu tsananin zafi suka zubo mata laɓɓanta taa ciza cikin yanayi na takaicin zuci da ciwon rai ta shiga fadin. "Allah na tuba Allah ka yafe mani laifinukana in har sanadin haka ka jarabe ni da wannan kaddara na gode Allah ka yafe mani". Wani kuka ne ya kwace mata ciki karfin hali ta shiga kokarin mikewa amma ina ta kasa komawa tayi ta zauna gami da jingina da bango tana mai runtse idanu zuciyarta take ji tana kartawa kanta na sarawa cikin wani irin tashin hankali wai ita ce yau 'yar cikinta ta dauko mata abin magana abin da za ayi tur! da ita da zuri'arta abin da zai bi duk wani nata ana tsine musu ita kam! ya zatayi da wannna rayuwar Hafsat ta gama da ita ta gama kashe mata rayuwa. "Kiyi Hakuri Zainabu ki dauki komai a matsayin rubutun ALKALAMIN KADDARA a gareki". Wani murmushi tayi mai ciwo tare da duban Goggo da tayi wuki-wuki kamar wacce tayi wa sarki karya ta kau da kai. "Umman Mariya in ban yi hakuri ba ya zan yi cuta ce an gama cuta ta ba yarda zan yi wai ace ni ce yau 'yar cikina ta dauko min magana ni dai na san ban yiwa iyaye na haka ba sannan ban cutar da 'ya'yan wasu ba ban zalunci mijina ba". Girgiza kai ta ke yi domin ita kadai ta san tashin hankalin da take ciki ji take yi kamar ta hadiyi zuciya ta bar duniyar nan.. *Kamala Minna*😘😘😘 [10/18, 3:06 PM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU BALA'I NA. KAMALA MINNA. *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA HAMSIN DA BAKWAI. Takure take waje daya sai fama rusar kuka take yi idanuwan nan nata sunyi luhu-luhu kamar wacce aka watsawa barkono zuciyarta take ji tana zafi gami da raɗaɗi wai ita ce Huzaif yayi wa haka mutumin da ta baiwa duk yardarta da kaunar ta ta mika masa duk wata ragama ta rayuwarta ta amince dashi ta yarda dashi amma yau ita ce yake daga hannu yana mari yana kiran ta jahila mahaukaciya kaicon wannan rayuwar. Kuka ta sake rushewa dashi tana dukan cikin ta kamar wata sabuwar hauka Goggo ce tashigo a daidai wannan lokacin ganin abin da take yi ya sanya ta kurma ihu ta isa gareta tana rirrike ta. "Haba Hafsatu kalau kike kuwa me ye haka kikayi?". "Goggo ki bar ni kam ki kyale ni wai ni Huzaif zai ciwa mutunci har da duka akan layi akan gaskiya". "Kiyi shiru nace miki ki kyale shi wallahi Allah sai ya gane bashi da wayo sai ya shaki bakin ciki kamar yarda ya shaka miki...". Abulle ta dago labulan dakin ta shigo fuskarta da wani murmushi wanda yafi kuka ciwo hannu ta harɗe a kirjin ta sai da ta kare musu kallo kafun ta nisa zuciyarta na kara suya. "ai in har mutum yace son zuciya zai biyewa to tabbas yana tare da tsintar kan sa cikin takaicin rayuwa Goggo da ma kin dai cewa zaku dauki mataki ai aikin gama ya rigaya ya gama mai yayi saura sai ta zauna a yarda take so ba dai haka ta zabawa rayuwarta ba ita ba wanda ya isa yayi mata magana ta dauke shi mutumin kirki ita sai dai ta zauna tayi son ranta to ai gashi nan ta gani a kwanon ta ba zan yi miki baki ba Hafsat amma za ki ji a jikinki da kuma duniyar rayuwarki ai duk wanda ya dama haka zai sha". Rushewa da kuka Hafsat ta sake yi tana rike kanta da take jin yana barazanar tarwatse wa ba abin da ke ci mata rai da tura mata bakin ciki sai yarda Huzaif yayi mata sosai zuciyarta take suya da kuna sosai take jin zuciyarta na sake buɗe wani fili mai girman gaske wani irin mahaukacin so taji na kawo mata farmaki a zuciyarta mikewa tayi idanuwanta a runtse sai faman tagaɗi take yi kamar wacce ta kora kayan maye. Da sauri Goggo Marka ta mike ganin tana kokarin ficewa daga dakin riko ta tayi tana mai cewa. "Ina kuma zaki cikin wannan yanayin..". Bata idar da maganar ta ta ba ta fizge hannunta tana mai duban Goggo bayan ta buɗe idanuwanta hawaye sai ambaliya suke yi. Hakan ba karamin kara batawa Abulle rai yayi ba ganin yarda Hafsat din tayi wa Goggo kamar wata tsaranta mikewa tayi cikin tsananin bacin rai lokaci guda ta fidda hannu ta dauke ta da mari ji kake tas! ta sake kifeta da wani barin tayi tangal tangal tana kokarin faduwa dafe da kuncinta. Duban Abulle ta shiga yi idanuwan ta buɗe sosai zuciyarta take zafi da wani irin raɗaɗi ga wani abu mai girma da taji ya tokare mata makoshi. "Banza maras hankali wanda bata san ciwon kan ta ba Allah ya wadaran naka dai ya lalace wallahi ki ko kunya ba kiji ba ko nadama ba za kiyi ba akan abin da kika dauko wa rayuwarki...ko da yake na lura har yanzu ba ki san ke wacece ba shiyasa amma akwai rana na nan zuwa zaki san Annabi ya faku". Bata tsaya sauraron jin kalaman Abulle ba ta bankaɗe labulan dakin ta ficewarta cikin tsananin tashin hankali mai girman gaske. Kuka ne ya kwacewa Abulle da baya da baya ta ja ta jingina da bango zuciyarta sai faman kartawa take yi gabadaya al'amarin Hafsat ya bata tsoro yanayin da ta ga tana kallon ta yayi matukar caza mata kwanya ba ta san ya akayi ba bata san har yaushe Hafsat ta zama haka ba tana mata magana amma yanayin kallon da take mata gabadaya ba wani alamun tsoro ko runsunawa a matsayin ta na mahaifiyarta anya kuwa ba laifi tayi wa Allah mai girma ba ya jarabe ta da Hafsat?. Girgiza kai ta shiga yi ranar da take tsoro kenan a rayuwarta ranar da Hafsat zata so fin karfin ta a duniyar nan ba abin da ke daga mata hankali ya hanata natsuwar rayuwa kamar Hafsat duk cikin 'ya'yanta ita ce kangararriya kuma Allah na gani ba wacce ta zama sanadin komai sai Mahiafiyarta sosai abin ke taba mata zuciya tayi fadan tayi rarrashin amma ina ta nuna bacin ranta sai ma ake nuna tsanar 'yarta take yi kaicon wannan rayuwa. Dago kai tayi ta dubi Goggo dake zaune bakin gado ta zabga tagumi kallo daya zaka yi mata ka gane kamar abin bai wani ɗaɗata da kasa ba amma akwai alamun sanyi a jikinta musamman yarda ta ga Abulle ta shiga yanayin tashin hankali. "Abin da nake ta faman tunasar dake kenan Goggo amma kin kasa gane wa Hafsat mace ce abu kalilan ne zai bata mata rayuwa sangartar da kike nuna mata da wai sunan so ne wallahi BA SO BA NE domin ba in da zai kai ta yanzu mai gari ya waya don Allah Goggo yanzu in wannan abin yafita mai kike zaton zai faru na rantse da Allah ko ruwa gagararmu sha zai yi". Gyaɗa kai kawai Goggo take yi tana faman turo baki gaba. "Ai da rufe ni da duka kikayi shine zan san na bata miki rai ko kuma ni na saka Hafsat dauko mana magana a duniyar nan ai ba wanda ya kai ni bakin ciki kan wannan lamarin kuma ai ba kanta farau ba balle ta zama karau uban kowa yana da nashi kashin a gindin sa don haka ban ga wanda zai takura wa Hafsat ba akan abin da tayi ai ba da gangan tayi ba Yaudaren ɗa namiji ne ta gamu da ita da kuma makircin wadancan mutanen...". "Goggo!". Abulle ta fadi da muryar sauti don maganar tayi matukar tunzura mata zuciya da sauri ta mike ta dubi Goggo ji take yi kamar ta daura hannu akai ta kurma ihu ko ta samu saukin wahalar zuciya da zafin ruhi da take ji. "Goggo ni ban ga amfanin daukar hakkin wanda ba su da laifi ba kuma na rantse da Allah in har kika ci gaba da tsanar su Mariya da uwarta wallahi sai hakkin su ya kama ki domin na lura a duniyar nan ba wacce kika tsana kamar ita duk biyayyar da take miki da cin kashin da kike mata ba ta taba daga kai ta dube ki ba tunda ta shigo gidan nan abun dai daya ne matsalar ki take fama da ita kullum ba ta da sauki anya kuwa rayuwa za ta yuwu a haka". Tana gama fadin haka ta juya da sauri ta fice daga cikin dakin cike da tashin hankali mai girman gaske bata san ya za tayi yanzu ba bata san mai ya dace tayi ba ta san dai Allah kadai ne zai yi mata maganin matsalar ta Allah na gani bata da laifi ta san ƙaddara ce kuma ta ansa da wannan tunanin zucin ta fice daga cikin gidan zuciyarta na harbawa da yarda zata tunkari mijinta da wannan al'amarin domin kuwa ya jima yana cewa Hafsat ta dawo gida amma ba yarda ta iya ta nuna masa yayi hakuri ba wani abu tun yana hakurin har yawan maganganun da ake yi akan Hafsat ya fara tunzura shi to ina ga yanzu yaji wannan bakin labarin. **** Hafsat kuwa tun da ta fice daga cikin gidan ta dau hanya zuciyarta sai an gizata take yi akan kawai ta tafi gidan su Huzaif domin ba za ta iya zama ba a halin da ake yanzu dole ta je ta same shi duk wacce za a yi sai dai ayi domin kuwa sosai take jin wani mahaukacin son sa na kara nakarkar mata da zuciya yana bubbuɗe mata duk wani sashi na jikin ta yana samun matsugun ni sosai take ta jin ta a tashin hankali wanda tun da take a rayuwarta ba ta taba zaton haka ba yau rana daya gabadaya komai ya kwance mata. Kuka sosai take yi na zuciya domin hawayen sun ki zubowa tashin hankalin dake kara rikita ta shine yarda mahaifiyarta take kallon ta ta tabbata in kowa zai yi mata uzuri ban da mahaifiyar domin ita kadai ne ta san halin da ta tsinci kanta a ciki a daidai wannan lokacin. Tafiya sosai tayi wacce akaran kanta ba ta san tayi taba ita dai ta san jefa kafafuwanta kawai take yi a in da taji sun sauka har izuwa lokacin da ta isa inda take zaton gidan su Huzaif ne sosai gaban ta ya shiga faduwa ba ta san mai zata ce ba bata san ya zata kalli mutanan gidan ba shin zuwa zata yi ta ce musu ɗan su yayi mata ciki ko ya ya. Girgizai kai ta shiga yi zuciyarta na faman harbawa tsoro da fargaba duk suka dire mata lokaci guda numfashi ta ja kafun ta dubi tankameman Get din gidan a hankali ta kai hannu ta shiga kwankwasawa daga can ciki taji motsin ana zare sakata mai gadi ne ya leko ya dube ta sama da kasa ganin ta a hargitse alamun akwai abun da ke damun ta hakan ya sanya shi tambayarta ko lafiya?. Hawaye ne suka balle mata da sauri ta dauke su sannan ta ce. "Don Allah wajan mutannan gidan nan na zo wajan Mahaifiyar Huzaif". Sake kallon ta yayi sama da kasa kafun ya ce. "Ko lafiya kike niman ta?". Runtse idanu tayi domin ita dai bata san abin da za ta ce da shi ba a halin da take yanzu in zai bar ta tashi kawai ya barta. Gefe ya ja alamun bata hanya don ya lura tana wani mataki na tashin hankali a hankali ta shiga share fuskarta sannan ta saka kafar cikin gidan tana takawa zuciyarta na kara curewa waje guda tayi tafiya kadan ta ja burki ta tsaya a tsakar gidan tana mai da numfashi tunani kawai take yi ta yarda zata shiga gidan nan ba ta san a wani matsayi zata je ba ita kanta ya gama kulle. A hankali ta shiga jan kafafuwanta tana mai da numfashi har ta isa babbar kofar da zai sadata da cikin falon Handle din ta rike ta murɗa idanuwanta a runtse gabanta na tsanarta bugu jin kofar ta buɗe ya sanyata tura kanta gaba gadi domin ta sadakar duk abin da zai faru sai dai ya faru. Zaune suke kowannan su fuskarsa a cure da alamun bacin rai motsin shigowar da akayi ne ya sanya macen dake tafaman sababi ta tsagaita gabadayan su suka juyo suna duban Hafsat da tayi wiki-wiki kamar wacce tayi wa sarki laifi Huzaif da ke zaune can gefe yana ta faman kumbure-kumbure ganin Hafsat da yayi kamar daga sama bai san lokacijln da ya mike ba cikin yanayi na firgici da tashin hankali yana nunata da hannu bakin sa sai rawa yake yi. "Ke! Uban me ya kawo ki gidan nan ban ce karki sake kokarin shigowa rayuwa ta b...". Tun kafun ya idar yaji saukar lafiyayyan mari yayi taga taga kamar zai fadi kasa hannunsa saman kuncin sa runtse idanu yayi kafun ya buɗe su akan mahaifin sa da ke tsaye yana ta faman huci da hannu ya nuna shi bakin sa na rawa magana yake kokarin yi amma ya kasa tari ne ya sarke shi da sauri ya dafe kirjin sa ya koma ya zauna gami da runtse idanu a hankali tarin ya laɓa amma bai buɗe idanuwansa ba zuciyarsa yake ji tana faman zafi bai san abin da ke damun Huzaif ba gabadaya ya rasa gane kan sa sosai yake fuskarta matsala akan ɗa daya tak! da yake dashi. "Ya akayi baiwar Allah?". Maihaifiyar Huzaif ta fadi tana duban Hafsat da izuwa lokacin ta fara dana sanin zuwa gidan su Huzaif idanuwanta su ka kawo ruwa sosai hannu ta saka ta dauke su ta fara kokarin yin magana da sauri Huzaif yayi tsalle ya dire gabanta yana famam tunkuɗata waje ita kuwa ta ki tafiya mahaifiyarsa ce ta iso ta riko hannun Hafsat ta dube ta cikin yanayi na rashin wasa. "Na san ɗana zai iya yin komai don ya cutar dake tunda na ganki cikin wannan halin na tabbatar akwai abin da yayi miki ki faɗa min na rantse miki zan bi miki hakkin ki kuma daga kan ki zai gane hakki ba wasa bane da yake ganin daukarsa ba komai bane". Sosai Hafsat taji wani iri gabanta ne ya shiga faduwa tunanin take yi ta fadi kowa yaji in ta fadi tana da tabbacin zata iya samun abin da take so kuma zata iya rasa wa sannan in taki fadi ta tabbata Huzaif zai yi nasara a akanta. Bakin ta na rawa hawaye na mata zuba sosai ta dubi Huzaif girgiza mata kai yake yi yanayin sa lokaci guda ya sauya tsoro sosai ya bayyana a fuskarsa kau da kai tayi jin yarda zuciyarta ke kokarin tausaya masa da yanayin da yake ciki sosai take jin GURBIN SO da ta bashi yana kokarin rinjayar haushin sa da take ji. "Uhmm dama...kawai dai". Sai kuma ta shiga taba cikin ta tana runtse idanu. Mutuwar tsaye Mahaifiyar Huzaif tayi ta shiga ambaton innalillahi wa inna ilahiri raji'un shi kuwa mahaifinsa da ya buɗe idanu lokacin da ya ji Hafsat ta fara magana ganin abin da take nuna wa ba karamin kaɗa 'yan hancin sa sukayi ba mikewa yayi cikin tsananin bacin rai da kunar zuciya. "Ke muje ki kai ni gidanku yanzun nan Hajiya maganar gaskiya Huzaif na lura aure yake so kuma wallahi in har ina numfashi a doron kasar nan wannan lamarin shine na karshe wanda zai dauko mani ya hanani kwanciyar hankali wallahi tallahi kin ji na rantse sai Huzaif ya auri wannan yarinyar ko da kuwa hakan na nufin numfashin sa zai yanke daga lokacin da na saka limami ya daura musu auren". Yana gama fadin haka ya fizgi hannun Hafsat yayi waje da ita ba Mahaifiyar Huzaif kadai ba hatta shi kasan din mutuwar tsaye yayi domin bai taba zaton hakan ba duban sa tayi fuskarta da murmushi mai tafe da hawaye ta juya cikin sauri tayi sama shi kuwa kwakkwarar motsi kasawa yayi kan sa ya ji yana juya masa lokaci guda yasaka hannayensa duk biyun ya dafe shi gabansa na tsananta faduwa wani firgici yaji shi a ciki musamman akan furucin mahaifinsa wanda ya tabbatar ai iya tabbata.... *KAMALA MINNA*😘😘😘😘 [10/18, 5:01 PM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU BALA'I NA. KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA HAMSIN DA TAKWAS Ba karamin tashin hankali Hafsat tashiga ba lokacin da taji mahaifin Huzaif yana ta faman sababi tun da suka dauko hanya ko hadiyar yawu ba yayi idanuwansa sun kaɗa sun yi jajir kamar jan gauta ita kan ta tayi dana sanin zuwan ta gidan. "Ban dan dakikan ci kina 'ya mace har ki zauna namiji ya yaudareki da banzayen kalaman sa ya nemi kashe miki rayuwa a banza a wofi bayan ke kan ki in mai tunani ce ya kamata tun kafin haka ta faru in son ki yake yi tsakani da Allah sai ya fito kuyi aure duk uwar da za kuyi ba wanda zai hana ku amma da yake kan ki a tukunya yake kika saki baki kika aminci da zancen Huzaif wanda ni kaina mahaifin sa Allah na gani ina fargaba akan sa da halayen sa ban san abin da yake damun ku ba 'ya'ya mata a yanzu da yawan ku maza na amfani da ku wajan saka muku son su wanda zai hana ku ganin laifin su sam! wasun ku basa gane SON GASKIYA da SON SHA'AWA". Kwaɓa yayi gami da dukan sitiyarin motar sai faman jan tsaki yake yi kamar zai tsinke harshen sa. Numfashi ta ja gami da haɗiye wani abu da taji ya tsaya mata a makoshi lokaci guda zufa ta shiga karyo mata sosai ta tsorata dashi ji take yi kamar tace ya tsaya ta sauka amma ina ta kasa. Cikin wannan yanayin da kwatancen da take masa suka iso kofar gidan parking yayi sannn ya juyo ya dube ta ganin tayi wiki-wiki da idanu ya sanya shi galla masa harara domin shi dai ba ya ganin laifin maza kamar yarda yake ganin laifin mata domin ba yarda za ayi kina 'ya mace har ki bari namiji ya yaudare ki ba tare da yardar ki ba in har kika nuna masa ba ki yarda ba ai ba dole zai yi miki ba ai so ba hauka bane. "Maza ki je kiyi mani sallama da mahaifin ki". Ware idanu tayi gabanta ya yanke ya fadi ita a rayuwarta har mantawa take yi tana da wani mutum wai mahaifi sosai taji wani irin yanayi a zuciyarta yau rana daya taji takaici rashin baiwa mahaifinta lokacin sa yau ga ranar sa ta zo shin da wani idanu zata je ta dube shi bata je masa da kayan alheri ba sai na akasin sa ta san dai ba zata fara ba don ta san izuwa wannan lokacin labari ya kai kunnansa. "Dake fa nake ko ba nan ne gidan naku ba?". Mahaifin Huzaif ya katse ta da sauri ciki firgici har tana buge koshin ta a jikin motar ta buɗe murfin ta fito sai faman rarraba idanu ta ke yi sosai ta lura da mutanan layin na ta kallonta da wani irin yanayi ita kanta sai ta ji ba dadi ba yarda ta iya haka ta ja kafafuwanta ta nubi cikin gidan kirjinta na dokawa da tashin hankali. A tsakar gida ta tadda Mariya na wanki kallo ta bi ta shi kafun ta kau da kai ita kan ta Mariyar kallon ta take amma bata ce da ita komai ba sai yanayim tausayi da ya bayyana a gareta sosai ta lura da abin da take zargi din da gaske din dai cikin ne domin gashi nan har ya fito don ita da duk ba ta lura ba. Hafsat na shiga cikin dakin ta tadda Goggo Marka zaune tallaɓe da haɓa abin duniya duk yabi yayi mata yawa ganin Hafsat ta shigo ya sanya ta mikewa cikin hanzari. "Ke kuma ina kika je cikin wannan halin so kike yi jama'a su fuskanci halin da kike ciki ne?". Kau da kai tayi tare da cizon laɓɓa ba tare da tace da ita komai ba. "Dake nake Hafsat kika yi banza dani". Turo baki tayi tare da cewa. "Zuwa nayi gidan su Huzaif na sanar da iyayensa yanzu haka tare da mahaifin sa nake domin yace sai ya zo ya sami mahaifina". Gaban Goggo Marka ne ya yanke ya fadi lokaci guda idanuwanta sukayo waje ta daura hannu akai. "Mun shiga uku in mahaifin ki ya san wannan lamarin ai mun boni". Dubanta Hafsat ta shiga yi ganin yanayin da ta shiga takaici ya sake kume ta. "Yana waje fa yana jira don cewa yayi nayi masa sallama da mahaifina". Da hanzari Goggo Marka ta figi zanin dake rataye ta yafa tayi waje zuciyarta da wani kudiri da ta dauka cikin kankanin lokaci har tuntube take yi wajan saurin tana fita hango shi tayi jikin motarsa ganin hakan ya sanyata tsayawa tana tunanin kafun ta canza fuska ta isa gareshi sam bai lura da ita ba sai ji yayi an bubbuga masa jikin mota da sauri ya juyo ya dube ta ganin ta ya sanya shi rinsinawa yana gaishe ta mai makon ta amsa sai ma wani wulakantaccen kallo da ta watsa masa. "Ina tsinannan ɗan naka ma ci amana Allah ya wadaran ɗa irin naka". Duban ta ya shiga yi domin jin maganganun nata yake yi kamar ba gaske ba sai da ya sake dubanta sosai yaga yarda take faman kallon sa a wulakance ya bashi tabbacin kila ita ce mahaifiyar Hafsat sosai yaji ɗacin maganar da tayi a ransa amma sai yaki nuna mata tunda a girme ta girmeshi. "Ayi hakuri Baba kin san sha'anin 'ya'yan namu na wannan zamanin ka haife su ne baka haifi halin su ba...". "Ni rufe mani baki kaji ko ai dole kace haka tun da ɗan ka ya gama da jikata ya cuce ta maganar gaskiya ba zan yarda ba dole kasan abin yi tun kafin wannan abin kunyar ya bazu a jama'a su sani don wallahi ba zan lamun ta ba". Duban ta yake yi da mamaki yarda ta hakikance tana ta faman zabga masa magana kamar shine yayi wa 'yarta ta ciki ko ya ce jikarta kamar yarda ta fadi ba zai yi mamaki ba lura da yayi ita tsohuwa ce kuma zai yarda da cewa RIKON KAKA bai yi ba don ya tabbata in da a hannun iyayenta wannan yarinyar take hakan ba zai taba faruwa ba in har sun san abin da suke yi. "Ayi hakuri Baba ina mahaifin ta yake". Wani irin dokawa gabanta yayi jin ya ambaci mahaifin Hafsat yake nema nan da nan jikin ta ya shiga rawa da sauri ta dube shi. "Baya nan Allah yayi masa rasuwa...kasan abin da za ayi kawai asirinmu a rufe ni da kai da 'ya'yan namu a zubda cikin nan tun kafin kowa ya sani ina ga haka shine mafita garemu...". "Zubar wa kuma bayan laifin da aka aikawa ubangiji sannan a sake yin wani laifin anya kuwa kina tausayin jikar nan taki anya kuwa kina son ku rabauta ke da ita to a gaskiya ba za ayi haka dani ba abu daya zan iya yi muku shine na aurawa jikarki ɗana ni nayi wannan alkawarin sannan ba za ayi auren ba har sai ta haife abin da ke cikinta ina ga wannan shi kadai ne mafita a garemu". Duban sa Goggo ta shiga yi cikin wani irin yanayi na rashin baiwa maganar tasa muhimmanci. "In kuwa haka ne sai dai ta koma gidan ku da zama don Allah na gani ba zan zauna da ita a zo ana zunɗena da gulma ta ba". Mamaki ne ya sake turnuke shi yau ya kara tabbatar da sakaci da rashin alfanun rikon kakan musamman ga 'ya'ya mata yanzu mai gari ya waya anya kuwa iyayen yarinyar nan sun san halin da 'yar su take ciki kuwa? Sosai yaji haushin yarda take maganganun ta don haka ya dube ta. "In har ba zaki yarda da abin da nace ba sai dai kowa ya kama gabansa don ba damuwa ta bace jikar ki ce zata shiga cikin gagarin rayuwa ina ma laifina akan kokarin da nayi". Yana gama fadin haka ya fada cikin motarsa ya ja ya tafi ya bar Goggo Marka sake da baki sai faman sababin take yi ganin mutane sun fara dawo da hankalin su gareta ya sanyata juyawa ta na fadin. "Aifa na kurya masu gansa kuka a idanu an bazo mani". ***** Abu kamar wasa lamari sai kara rincaɓewa yake yi a wajan Hafsat tun ranar da mahaifin Huzaif ya zo ko kafarsa ba ta sake gani ba sannan ga Goggo Marka ta saka ta gaba a na cikin haka mahaifinta yayi wa gidan tsinke ba karamin kaɗuwa tayi ba ita da Goggo Marka idanuwansa sun kaɗa sun yi jajir kallo daya za kayi masa ya baka tausayin don tashin hankali iyakar karshensa ya shiga cikin sa duban Hafsat yayi. "Ni Mahaifin ki ne amma daidai da rana daya ba ki taba bani wannan matsayin nawa ba Hafsat ni na haifeki amma ni da banza duk daya ni da uwarki ba wanda kike gani da gashi rayuwarki kike yi yarda kike so baki da mai kwaɓa ko ma an kwaɓe kin Goggo gani take yi kamar matsa miki ake yi yanzu wa gari ya waya iyee ke ba ki cikin kwanciyar hankali mu iyayenki da mu ka san kina da hakki akanmu mu ma ba mu da kwanciyar hankali yanzu uwarki na can bata da lafiya kuma ba wanda ya zama sanadi sai ke". Wasu hawaye masu dumi suka zubo masa kau da kai yayi cikin dauriya. "Hafsat tunda kika taso a matsayin ki na 'ya mace mai rauni mai makon ki yi kokarin tsare rayuwarki amma ki ka ki kika nuna ba wanda ya isa dake ke a tunanin ki wannan rawar kai da kike yi shi zai sa an gan ki da mutunci kina tunanin wannnan rayuwar da kika daukarwa kan ki akwai na mijin da zai gan ki da mutunci har yace zai iya zama dake a matsayin matar aure ina! ba wani ɗa namiji da zai auri jahila ko wani namji burin sa ya samarwa 'ya'yansa uwa ta gari ke ba abin kwaikwayo bane ga 'yar uwarki ba abin da ba kuyi mata ba ba abin da ba ku ce mata ba akan neman ilmi da take yi haka kuke jifan ta da mugayen kalamai yanzu wa gari ya waye ke da ita waye yake da nasara a rayuwarsa na tabbata yanzu Mariya duk wani namiji mai hankali mai natsuwa zai so ace ta zama matarsa amma ke fa a yanzu kina tunanin ko wanda yayi miki wannan aikin zai aure ki ne ina! ko ma ya yarda zai aure ki to wallahi ba zai taba ganin ki da mutunci ba ke da banza duk daya zai dauke ku". Goge hawayen da suka zubo masa yayi gami da girgiza kai. "Yanzu kika fara shiga tashin hankalin rayuwa in har kika ce ba zaki sauya ba". Yana fadin haka yafice zuciyarsa cunkushe da tashin hankali. Goggo Marka dake can gefe tun dazu tayi wiki-wiki da ita duk abin duniya yabi ya dame ta ta rasa me za tayi maganar tun tana boye wa har an fara ganowa duban Hafsat tayi. "Hafsat wai me ya kamata muyi ne yanzu don ni gaskiya na fara tsorata da lamarin ko gidan iyayen naki zaki koma?". Wani duban rashin fahimta Hafsat tayi mata zuciyarta na zafi me Goggo marka take nufi da wannan maganar ta ta da take fadi girgiza kai tayi cike da kunar rai. "Kamar ya na koma gidan iyayena Goggo kina kallon fa abin da Babana yace sannan kuma kice na koma bayan ba a gabansu komai ya same ni ba". "To ya kike so in yi ne kowa ya zo kaina zai sauke matsalarsa kamar a kai na ne wannan lamarin ya fara faruwa ni gaskiya na gaji gwanda ki koma gaban iyayenki ko kuma kisan yarda zakiyi ki sami Huzaifa din akan maganar auren ku da mahaifin sa ya zo dashi". Hawaye ne suka shiga zubo mata cike da takaicin yarda Goggo Marka ke nuna mata ta fara gajiyawa da ganin ta mikewa tayi sai faman tangaɗi take yi ga cikin nata ya bayyana sosai. "Ni Goggo kike hantara ni kike cewa kin gaji da ganina kenan dama ba son Allah kike yi mani ba dama kin rabani da iyayena ne don ki bata min rayuwa". Gyaɗa kai ta shiga yi hawaye na sake balle mata. "Shikenan Goggo amma ki sani wallahi ba in da zani domin ba laifin iyaye don haka ba zai je na kara tayar musu da hankali ba a nan zan zauna in ma haihuwar ce sai dai nayi ta a nan sai dai duk abin da zai faru ya faru". Ta karashe tana galla mata harara cike da takaici Mikewa Goggo Marka ta yi ta iso gareta. "Hafsat ni kike fadawa wannan maganar haka?". "An fada miki kin cancanta ne shiyasa kuma wallahi takaicin nan tare dake za mu shanye shi". Mamaki ne ya cikata ganin yarda Hafsat ke mata magana cikin tsawa-tsawa kamar zata kai mata bugu bata gama shan mamaki ba sai da ta ga Hafsat ta tsartar da yawu ta bankaɗe labule ta fice daga cikin dakin. *Kamala Minna*😘😘😘 [10/19, 9:42 AM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU BALA'I NA. KAMALA MINNA. *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA HAMSIN DA TARA Runtse idanu tayi daidai lokacin da ya isa inda take tsaye kwankwarar motsi ta kasa yi zuciyarta sai faman harbawa take yi kamar zata faso kirji ta fito waje kwanyarta take ji tana yawo dauke da wani irin hayaniya mai kama da saukar a radu buɗe idanunta tayi a karo na ba adadi ta sauke a saitin inda fuskarsa take sai faman sauke mata wani shu'umammen murmushi yake yi wanda yake kara rikita mata duk wani tunani nata da natsuwarta. Bata san ya za tayi ba zuciyarta gabadaya ta gama tafiya a duniyar Dr.karami lokaci mai tsayi tayi kokarin kwatar kanta amma abin ya ci turo sai ma abin da ya cigaba sosai take jin zuciyarta na kara matsewa da kaunarsa kaunar da take jin ta tana kara hayayyafar 'ya'ya wanda ba za ta iya cewa ga adadin su ba kaunar ce zallarta ba tare da hadi ba wanda ta jima da AMANNA akan haka kaunar Dr.Karami kamar halitta ce da Allah yayi mata tun lokacin da zai busa mata numfashi. Wani numfashi ta sake ja a daidai lokacin da taji takunsa na kusantowa gareta yana kara sautin bugun zuciyarta ko wani sashi na jikinta take jin yana narkewa kafafuwanta jin su take yi kamar ba za su dauke taba. "Mariya!!!". Ya fadi da wani irin sautin da ya sanyata sumar tsaye gami da sadakarwa zuciyarta ta tarwatse da sautin zazzakar muryarsa mai dauke da wani sirrin mai kokarin fallasa sirrin dake boye a bayan zuciyarta. Buɗe bakinta tayi ta shiga kokarin buɗewa domin ansawa amma hakan ya gagara sai ma motsi da laɓɓanta suke yi amma ta kasa furta wata kalma wacce zata taimaka mata domin dawowa hayyacinta. Idanuwansa ne suka sarke cikin nata a bazata wanda hakan ya sagar mata da duk wata gaɓa ta jikinta wanda za ta taimaka mata wajan kwatar kanta daga barin kallonsa wani maganakisu take hangowa yana zabarin duk wani sirrin dake cikin idanuwansa yana sarkewa da nata. Wani yin kuri tayi mai tafe da numfashi ta kau da kanta tana faman ajiyar zuciya wani murmushi ne mai girman gaske ya bayyana akan k'yank'yawar fuskarta sai faman kaɗa kwayar idanuwanta take yi. Ba zato ko tsammani taga mutum ya durkushe a gabanta da sauri tayi kokarin ja baya amma sai taji kamar an kafe mata kafafu ne dago idanuwansa yayi ya sauke a saitin nata tare da kokarin kamo hannunta guda wanda ta rufe rabin fuskarta dashi. "Ina son ki Mariya zuciyata ta gama gajiwa so ne kawai a cikin ta yake zarge ko wani sashi da loko na cikin ta GURBIN SO da na baki wanda ya kasance ke kadai ce a cikin sa so nake yi ki bani damar da zan farfaɗo dashi daga sumar da yayi na wucin gani kice dani kina so na zan zamo ABOKIN RAYUWA a gareki". 'Yaa Rabbi!!". Ta fadi cikin bugun zuciya kankame jikinta tashiga yi domin ta rasa me zata yi ta rasa ma a wata duniyar take a wannan halin ta kasa sarrafa kanta gani take yi kamar ba ita ba gani take yi kamar wata Mariyar ce ba ita ba wai Dr.Karami akan gwuiwowin sa yana neman SO gareta shine yake fada mata kalaman da suke kokarin tarwatsa mata zuciya da kwanya ba zata iya ganin sa a haka ba ba zata iya sakin kunnuwanta taji kalaman da yake fadi kanta yayi kadan ya dauka komai zai iya faruwa zuciyarta zata iya fashewa da kaunarsa kaunar da take hangota tafi duk wata kauna da masoya suke nuna wa junansu. Bata taba zaton zata tsinci kanta a wannan matakin ba bata taba zaton zuciyarta zata iya sakewa haka ba har ta saurari irin wannan kalaman... "Ki ce wani abu mana duniyar nan a yanzu mu kadai ne a cikinta karki bari kunya tayi miki SAGEGEDUWA ki fito fili ba wanda zai ganki ki kalle ni a matsayin ni kadai ne babu kowa ki kalle ni a a matsayin wanda shine a matsayin ABOKIN RAYUWA a gareki". 'Anya kuwa'. Ta fadi cikin zuciyarta da k'yar. Dan yatsarta na tsakiya taji ya kama gabadaya ji tayi wani irin Shock ya kamata duk wata kofar dake jikinta runtse idanu tayi tana mai jan numfashi kamar zata shiɗe da sauri ta shiga ambaton 'Yaa Ilahi!'. Kafun ta shiga kokarin kwatar kanta amma ina shigar zobe da taji cikin dan yatsar nata ne ya sanyata sakin jiki sosai ji da tayi ya sakar mata hannu ya sanyata ja da baya da sauri tana mai da numfashi buɗe idanuwanta tayi saitin hannunta da take ji kamar ba nata ba duban hannun nata tayi wani hadadden Zobe ta gani sai k'yalli yake yi ruwan Gold mai tsananin kyau da burgewa sosai taji wani iri a zuciyarta da saurin ta dube shi shima ita yake duba idanuwansa sun yi wani kala kamar ruwan Rose sai sheki suke yi. "Please My Pretty Say something to me?". Ya fadi da wata kwantacciyar murya wacce zata iya rantsewa ba tasa bane in ba don ta ganshi a gabanta ba sannan laɓɓansa na motsawa cikin wani irin salo wanda yake kara rikita mata tunanin kwanyarta. Hannun ta dago mai zobe a ciki ta shiga kallon zoben tana tabawa da dayan hannun nata wasu abubuwa taji kamar sako suna shiga jikinta a duk sa'ilin da ta murza zoben harufan dake jiki suke kara sanyata jin wani iri kyallin da suke a tare ne suke kara sanya zuciyarta son zoben. "Duniyar nan ina so ta zamo tamu mu kadai ki dubi duk girman ta da fadin ta ki saka a ranki mu kadai ne a ciki ba wani wanda zai fado cikin ta har ya so ba mu wata matsala". Dam! taji gabanta ya bugu jin furucin sa zuciyarta ne ta mikata wani mataki mai girma da nisa 'Dr.Aqeel' zuciyarta ta bankado mata runtse idanu tayi sosai wani sashi ya shiga kawo mata shi tana kara kamba mashi a gareta kai ta shiga girgizawa a hankali wasu hawaye suka tarun mata a GURBIN IDO bata so ba bata so abin da zai kara rikita mata rayuwa a irin wannan lokacin mai girman gaske a gareta tashin hankali take tsoro bata so a sake komawa gidan jiya so take yi duniyar ace ta cigaba da wanzuwa a wannan matakin da take ciki a yanzu amma bata tunanin haka zata kasance dole ta hakura dole ne... "Kuka!!!". Ta ji muryarsa kamar an hura sarewa gabadaya taji kunnuwanta sun dauka kwanyarta ta dau sautin sosai ji tayi tana yawo kamar zata zube a kasa. "Mariya kukan me kike yi haka...fada min please ko na ɓata miki rai ne?". Yanayin yarda yake maganar ya kara narkar mata da zuciya a tausayin sa ta sani tana son sa amma bata san yarda zatayi da Dr.Aqeel ba shima yayi mata HALACCI bata so ace ita tayi masa BUTULCI girgiza kai ta shiga yi. 'Ba yarda zaki yi dole ki zaɓi daya don mace bata auren NAMIJI sama da daya'. Zuciyarta ta fadi mata hannayenta ta saka ta rufe kunnuwanta ji take yi kamar furucin zuciyarta da take kamar a bayyane yake. 'Dr.Aqeel'. Ta fadi a zuciyarta sai dai abin da bata sani ba shine maganar da tayi a bayyana take. Dr.Karami da ya tunkaro wajanta don rarrashi jin abin da tace ya sanya shi saurin jar burki yana mai watsa mata wani irin kallo mai cike da tuhuma da zargi lokaci guda ya ji zuciyarsa na harbawa da sauri-sauri runtse idanunsa yayi sannan ya buɗe akanta. Ita kanta a jikin ta taji yarda kallon nasa ke ɓulata hakan ya tabbatar mata akwai abin da tayi wanda ya sanya shi yi mata irin wannan kallon dago idanun ta tayi ta dube shi da sauri ta kau da kanta zuciyarta tayi wani irin dokawa. "Mariya da gaske kike abin da najiyewa kunnuwa na gaskiya ne?". Ya fadi muryarsa da zafi a cikinta wani iri taji jikinta nayi mata sosai ta gano laifin don haka da sauri ta shiga girgiza kai zuciyarta na rikicewa da tashin hankalin da ta hango a idanunsa sosai taji kanta na cakuɗewa yana mikata wani mataki wanda bata taba jin ta a cikin sa ba. "Karki ce mani shine kar ki ce mani zuciyarki na gareshi karki ce mani shine mai GURBIN SO a zuciyarki bani ba don Allah Mariya na roke ki karki buɗe bakin ki ki sanar da ni gaskiya ne na san karya kunnuwa suka jiye mani Please Don't say anything". Ya karashe cikin jarumtar zuciyarsa da yake jinta kamar zata tarwatse numfashi yake ja a hankali da sauri ya daga hannayensa duk biyun ya dafe kan sa da su wani irin juyawa yake jin kansa nayi kamar zai tarwatse gida biyu. Laɓɓanta ta tura cikin bakin ta tana cizawa kuskuren da take ji tayi take son ya zama a mafarki ba gaske ba ba za ta iya cigaba da kallon Dr.Karami a yarda take ganinnsa a yanzu cikin wani irin yanayi da take jin yana karta mata zuciya. "kai ne...". Ta fadi da kyar zuciyarta na yinkurawa kamar zata tarwatse hakan ya hanata karasa abin da tayi niyyar fadi. "Ni ne me Mariya fadi nine me don Alalh ki bude bakinki ki fadi naji ko zuciyar tawa zata rangwanta min daga ciwon da ta tsomani a ciki. Juyawa tayi da sauri tana kokarin barin wajan da sauri ya riko mata hannu ya matse sosai har sai da tayi kara mai dan sauti dubanta yake yi cikin idanunta da suka kaɗa sukayi jajir. "Ba zan sake ki ba har sai kin fada min matsayi na". "Ina son ka Dr.Karami kai ne mallakin zuciyata..amma ka sani ina tsoron butulci...". A hankali ya sassauta mata rikon da yayi mata wani murmushi na bayyana a saman fuskarsa ya shiga girgiza kai. "ba a so dole sannan kyautatawa daban so shima daban karki ce don Dr.Aqeel ya taimaka miki a rayuwa haka na nufin sai kin so shi a,a ban ce karki so shi ba amma ba wai wanda zai cutar dake ba ki ajje batun sa a gefe ki anshi SO na mu rayu tare". Girgiza kai take yi a hankali tana dauke hawayen da suke zubo mata maganar tasa take jin ta wani iri a zuciyarta da kwanyarta laɓɓanta ta shiga motsawa alamun son yin magana amma ta kasa sai murza zoben hannunta take yi. "Mariya!!". Ya ambata cikin wani irin yanayi mai tafe da mamaki da al'ajabi da sauri ta dube shi ganin yana kallon kofar gidan su ya sanya itama ta juya da sauri ware idanu tayi waje ganin Hafsat ta leko ko mayafi babu ga turtsetsen ciki a gabanta runtse idanu tayi kafun ta dubeshi zuciyarta na dokawa da sauri-sauri. Kallon tuhuma yake yi musu su dukan biyun kafun ya ja numfashi ya dubi Mariya wacce itama izuwa wannan lokacin ta dawo da dubanta gareshi kwalla ne suka kawowa idanuwanta farmaki da sauri ta hadiye su. "Me kenan Mariya me ke faruwa ne da Hafsat haka karki ce mani...". Shiru yayi cikin yanayin tausayi yana girgiza kai don ya tabbatar da zarginsa ganin yarda Mariya ta rikice. "Allah ya kyauta". ya sake fadi ganin Mariya bata da niyar cewa komai sake kallon Hafsat yayi wacce itama a daidai wannan lokacin idanuwanta na kansa kau da kai yayi cikin faduwar gaba da sauri ya juya ya koma cikin motarsa wata katuwar leda ya fiddo da ita ya ajje gaban Mariya kafin ya juya da sauri ya koma cikin motarsa zuciyarsa nayi masa zafi sosai. Sakin baki tayi tana kallonsa har ya ja motar bayan ya dago mata hannu ya wuce sannan ta sungumi ledar jiki a sanyaye tayi hanyar gida har zuwa lokacin Hafsat na tsaye bakin kofar ko motsi ba tayi ba. "Haba don Allah Hafsat haka da kike yi fa wallahi bai dace ba zubda mutunci ne kike yi duk wanda ya ganki a haka dole yayi miki wani kallo na daban". Gyatsi ne tayi kafun ta kalli hannun Mariya ta kau da kai. "Meye naki a ciki ko kina tsoron kar Dr.Karami yayi zargin duk daya ne". 'Allah yayi min tsari da aikata mugun abu irin wannan'. Mariya ta fadi da sauri cikin zuciyarta gami da raɓa Hafsat tayi shigewarta cikin gida zuciyarta da takaicin halin Hafsat duk da abinda ya faru da ita amma har yanzu ba za tayi karatun ta natsu ba ta saita rayuwarta sosai take jin bakin ciki da takaicin halin da Hafsat ta tsinci kanta sosai abin ke taba mata zuciya amma ita Hafsat ta kasa fahimtar ta na daukar da take yi mata na 'yar uwa ciki daya... *Kamala Minna* 😍😍😍 [10/19, 10:59 AM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU BALA'I NA. KAMALA MINNA. *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA SITTIN. Tunani kawai take yi akan yarda zata anshi Dr.Karami lokaci guda bayan kuma ta san akwai wani akasa ko da yake ya kamata izuwa wannan lokaci ta saukaka wa kanta domin samun natsuwar zuciyarta. Amma ta yaya hakan zai kasance ta yaya hakan zata faru bata sani ba bata san yarda zata dauki lamarin ba sosai take jin kamar bata kyautawa Dr.Aqeel ba in tayi duba da yanayin dake tsakaninta dashi. "So daban kyautatawa daban". Ta jiyo wani sashi na zuciyarta na dauko mata wani sashi na zancen Dr.Karami da ya faɗa mata. "Amma ai kyautatawa na haifar da so da kauna ga mutane biyu? Kuma ai kyautatawa na cikin abin da ke haifar da so ga zukatan dangin rai". Ta fadi tana tura laɓɓanta cikin baki tana cizawa a hankali juyi tayi daga kwance da take ta mai da idanuwanta suna kallon sama sosai take jin zuciyarta da kwanyarta na mikata wani mataki na musamman wanda zata so ace ta rayuwa a cikin sa har gaban abada amma kuma bata zaton haka ganin lamarin take kawai a labarin kanzon kurege ba zai taba tabbata ba. Numfashi ta ja tana mai da numfashe idanuwanta a hankali ta buɗe su ta dago dan yatsen hannunta wanda yake dauke da zoben da Dr.Karami ya sanya mata kallonsa take yi zuciyarta na kara buɗewa da kaunarsa ji take yi duk wani GURBIN SO na zuciyarta Dr.Karami yana kokarin mamayewa cikin yan kwanakin nan sosai take jin ta a wani mataki na farin cikin zuciya wacce ta cika da kauna zallarta. Zata so ace rayuwar ta mika a haka za ta so ace rayuwar ta cigaba da tafiya a haka amma ina! akwai wani wajan da za a kin tafiyar ta sani ALKALAMIN ƘADDARA zai iya zano mata wani abu mai girman gaske ya dora mata a matsayin JARRABI izuwa wannan lokaci ta rigaya ta saba sosai da sosai bata tunanin akwai kaddarar da zata fado rayuwarta bata yi kokarin ganin ta cinye ta ba. Gabanta ne ya doka da sauri ta mike tana ambatar 'Hasbunallahu wa ni'imal wakil Yaa Hayyu Yaa Kayyum'. Idanuwanta ta zaro sosai hannayenta saman kirjin ta tana jin yarda BUGUN ZUCIYARTA ke kara tsananta. "ME KE FARUWA?". Ta fadi tana jan numfashi da sauri ta shiga kokarin mikewa ji tayi duk ilahirin jikinta ya dauki sanyi kamar an doke mata duk wata gaɓa dake jikin ta a hankali ta shiga taka kafafuwanta kanta ko dan kwali babu yalwataccen gashin kanta ya baje sosai har zuwa fuskarta da sauri ta janyeshi zuwa baya ba tare da ta sanya dankwali ba tayi hanyar waje a bakin kofa ta tsaya tana ajiyar zuciya Umma ta gani zaune ta zabga tagumi da sauri ta isa gareta ta taɓa ta amma ba alamaun ta san ta zo wajan. "Umma!". Mariya ta fadi da sauti a muryarta tana mai jinjigata a hankali taja wani dogon numfashi ta dago idanuwanta da suka dan kaɗa ta dubi Mariya kafun ta kau da su cikin wani irin yanayi na damuwa. "Umma lafiya na ganki haka?". Murmushi kadan tayi wanda da ka kalle ta zaka gane na dole ne girgiza kai tayi tana cizon laɓɓa. "Mariya mahaifin ki shi na tuna wani mafarki mara dadi nayi a yanzu a nan zaune ina gangaɗi sosai naji na tsorata". Ware idanu Mariya tayi jin abin da Umma ta fadi ko dai wani abu na shirin faruwa ne domin itama taji irin yanayin a yanzu zuciyarta ta sake bugawa hannun Umma ta kamo ta danke sosai cikin nata. "Anya Umma Abbana ba ya cikin matsala zuciyata sosai take hasashen haka ina tsoro Umma ya kamata ace ko ina yake ya bayyana muna tsananin bukatarsa hakurinmu umma...". "Mariya to ya za muyi da ƙaddarar Allah haka ya tsara mana a rayuwa dole hakan sai ta faru fatana dai duk in da yake tsayin shekarun nan Allah ya bayyana mana shi". Hawaye ne suka kwaranyo wa Mariya a idanu da sauri ta saka bayan hannunta tana shafe su tana mikewa kan kafafuwan ta sosai take ji a zuciyarta mahaifinta duk inda yake baya cikin dadi da farinciki gami da kwanciyar hankali sosai take jin fargaba da tsoro a zuciyarta tana son ganin mahaifinta tana so ta sanya shi a idaniyar ta sosai take kewarsa. A kullum sai tayi tunaninsa tana son ta ganshi tana so ya dawo cikin duniyarsu su rayu tare zuciyarta sosai take zafi duk sa'ilin da ta tuna lokacin da mahaifinta ya bar su ciki mawuyacin hali ta sani kaunar da yake nuna musu ba zai sanyashi guje musu ba ta tabbata akwai abin da ya sanyashi barin su ya mika wani wajan tsayin lokaci mai girman gaske... **** Saukarta kenan daga Napep tana kokarin shiga gidan su Mariya taji anyi mata Horn bata yi zaton da ita ake ba sai da taji ana tayi ba ƙanƙautawa sannan ta juya ta kalli in ta tajiyo horn na tashi ta gefen idanu Dr.Aqeel ne tsaye kafarsa daya a waje daya cikin motar ware idanu tayi gami da juyowa tana duban sa ba tare da ta ce kala ba. A hankali ya kulle motar ya shiga takowa gareta harɗe hannayenta tayi a kirji tana kallonsa Up and Down cikin wani irin yanayi zuciyarta na suffan ta mata tsarin halintarsa na cikakken namiji wanda ya hada duk wani abu da mace ke bukata a wajan namiji sanye yake cikin kananun kaya suit light blue wanda tayi matukar yi masa kyau hannunsa daure da hadadden agogon Rolex mai tsananin kyau.... Da sauri ta ja numfashi sa'ilin da taji daddar kamshin turarensa ya daki hancinta da sauri ta kau da idanuwanta daga barin kallon sa. "Halin dai naki na nan na shan kamshi Baseera". Duban sa ta sake yi gami da murmushin gefen kumatu. "In dai ba mugun hali bane ai da sauki". Ta fadin tana kallon wani gefe daban. Nishin da taji yayi ne mai sauti ya sanyata duban sa da sauri cikin alamun tuhuma yanayinsa ta ga ya sauya gabadaya kamar wanda ba shi da lafiya laɓɓansa ya tura cikin baki yana cizawa. "Ban san mai zai ce miki ba Baseera na san kin fahimci halin da nake ciki akan ƙawarki ina son ta sosai zuciyata take dakon sonta ya kamata izuwa wannan lokaci ace ta bani dama son ta nake yi so zallarsa". Tunda ya fara magana take kallonsa da mamaki namiji har namiji amma so ya mai dashi wani iri kau da kai tayi zuciyarta na jin haushin yanayin da ta ga yana nunawa AKAN SO. "Dr.Aqeel kenan nifa wannan lamarin naku na rasa gane kan sa wallahi abu yaki ci ya ki cinyewa kun saka min ƙawata a gaba sai faman figarta kuke yi kun hanata sakat! bayan kuma ku kan ku kun sani ba yarda za ayi dukkanku ku aure ta dole sai dai daya a cikin ku". "Ni nake son ta Baseera amma ta kasa sanin haka". "Su ma sauran ai son ta suke yi ko ya dai kamata ace kun kafa teburin Sulhu a tsakanin ku ku barwa daya in kuma ba za ku iya ba gaskiya dole ku rabu da ita wani ya aureta daban tun da kun kasa hakurar da zuciyarku akan sonta". girgiza kai yayi yana jin yarda zuciyarsa ke kara buɗewa da son Mariya ya lura har yanzu Baseera bata san SO ba shi yasa bata dauki lamarin nashi da girma ba. "Zan kama kafa dake". "Ban yarda ba". "Saboda me?". "Ba zan iya bane gaskiya ba zan takura mata ba". runtse idanu yayi kafun ya buɗe su akan ta da wani rin yanayi kallon ta yake yi sosai da sosai zuciyarsa na mikashi wani mataki mai girman gaske kwanyarsa yake ji ta shiga yawo dashi wani sashi na daban tana buɗe masa shafi-shafin wasu lamuraka masu girman. "Zan takura miki". Ya fadi da wani irin yanayi a muryarsa ita kanta sai da taji tsigar jikinta ta mike numfashi ta ja. "Zaka iya takura mani amma bana tunanin takurawar taka za tayi amfani". "Dole tayi amfani ki rubuta ki ajje daga yau ina tare da ke har ranar da BURINA zai cika". ya fadi muryarsa da zurfi a cikinta dubansa tayi da murmushi a fuskarta. "MU ZUBA MU GANI". Ita ma ta fadi da murya mai sauti da sauri ta juya ta doshi kofar gidan gabanta na dokawa sosai taji a jikinta kallon ta yake yi sosai take jin kafafuwanta kamar za su zubda ita me Dr.Aqeel ke nufi da ita sosai taji wani iri a jikinta sosai take jin kamar wani abu na faru kwanyarta taji tana yamutsewa zuciyarta na matsewa tana mikata wani mataki mai girman gaske. Tana shiga cikin soron gidan ta jingina da bango tana mai da numfashi idanuwanta a lumshe sai da ta shafe dakiku kafun ta ja kafafuwanta da taji sun yi mata sanyi ta shiga cikin gidan. ba kowa a tsakar gidan hakan ya bata damar zarcewa bangaren su Mariya bakinta dauke da Sallama ba ansa ta ba haka ya sanya ta sake yin sallamar nan ma ba a ansata ba labulan dakin ta daga can ta hango Mariya rigingine a gado idanuwanta na kallon saman dakin da sauri ta zare takalman ta ta shiga cikin dakin ba tare da ta sani ba har ta zauna bakin gadon hannunta ta kalla zoben da ta gani ne ya sanyata ware idanu cike da mamaki ga dariya na kokarin kwace mata da sauri ta sanya hannu ta rufe bakinta sai da ta gama karewa zoben kallo sannan ta daka mata duka. A firgice ta mike tana shirin zurawa a guje ganin Baseera ya sanyata sakin jiki tayi kasa ta zauna tana mai da numfashi gami da dafe kirji. "Mtss Allah ya kyauta miki ai wannan sai ki firgita mutum ya zura da gudu". Dariya Baseera tayi gami da kamo hannun Mariya mai zobe ta kalla sannan ta daga idanuwanta ta kalle ta cikin tuhuma tana mai sakin murmushi hakan da Mariya ta gani ya sanya fizge hannunta ita ma tana dariya. "Mariya!!". Baseera ta fadi da murya mai zurfi kafun ta dafa kafaɗarta muryarta tayi kasa sosai. "Ya kamata zuwa wannan lokacin ki san matsaya a rayuwarki rayuwa baza ta taba daidai a wannan matakin ba da kike kai a yanzu kuruciyarki zaki duba karki yasar da ita a banza a wofi wajan sanyawa kan ki damuwa don Allah na roke ki Mariya ki san abin yi Umma za ki duba nasan ta fiki shiga tashin hankali akan wannan lamarin sai dai ba zata nuna miki hakan ba". Cikin rashin fahimta Mariya ke dubanta. "wai shin me kike nufi ne?". "Kin fi kowa sani Mariya akan maganar ki da wadannan mutanan ne ya kamata ki tsaida guda daya gwani kin ga yanzu haka Dr.Aqeel yana kofar gidan nan don na tabbata ya dade da zuwa a nan na tadda shi". Da sauri ta dafe kirji gami da zaro idanu waje. "waje fa kika ce Baseera na shiga uku". "Ba ki shiga uku ba zabi ne naki". Shiru Mariya tayi tana runtse idanu kafun ta riko Hannun Baseera. "Baseera akwai matsala akwai abin da baki sani ba wanda na boye miki maganar gaskiya ina tsoron yanayin nan da muke ciki kisan a halin yanzu Hafsat na nan dauke da juna biyu kuma Huzaif ne sila...". Fizge hannunta Baseera tayi ta mike tsaye jikinta har ɓari yake yi idanuwanta a warwaje laɓɓanta sai motsawa suke yi alamun tana son yin magana amma ta kasa numfashi ta ja kafun ta runtse idanu ta buɗe su. "me ki ke son ce mani Mariya Huzaif din da na sani Yaa Rabbi!". dafe kanta tayi gami da komawa ta zauna zuciyarta na matsewa da wani irin yanayi. "Garin ya ya hakan ta faru Mariya?". Girgiza kai ta shiga yi kafun ta ciji laɓɓanta. "Baseera Alfarma nake nema gareki". ta fadi tana kamo hannayenta Baseera da jikin ta ya gama yin la'asar ta sarke da nata tana faman matsewa zuciyarta na bugawa da wani irin yanayi mai girman gaske. maganar take ji tana yi mata nauyi maganar da take so ta fadiwa Baseera bata san ya zata dauke ta ba tana tsoron taki amincewa ba tana son wani abu na rashin jin dadi ya gilma a tsakaninsu in taji bukatarta ta dago idanunta tayi da suka kaɗa ta dubi Baseera wacce itama izuwa wannan lokacin gabadaya hankalinta ta mai dashi wajan ta idanuwanta na zagayawa a gareta tana jin yarda zuciyoyin su su dukan biyun ke bugawa da sauri sauri.... *Kamala Minna*😘😘😘 [10/21, 9:33 AM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU BALA'I. NA. KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA SITTIN DA DAYA. Numfashi taja mai zurfi kafun ta tura laɓɓanta cikin baki tana cizawa idanuwanta har zuwa wannan lokaci suna kan Baseera zuciyarta sai kara harɓawa take yi da sauri-sauri fargabarta da tsoronta suna kara daɗuwa sosai take hango rashin yarda da amincewa gami da rigima cikin idanun Baseera wacce tayi mata fakare tana yi mata kallon tuhuma. 'Ya za ta dauki lamarin in na sanar da ita anya kuwa zata yarda har ta aminci da bukatata?'. Mariya ta fadi haka a ranta tana kara matse hannun Baseera a cikin nata. "wai me ke faruwa ne?". Baseera ta fada gabanta ita ma na cigaba da faduwa. "Baseera ki Auri Dr.Aqeel". Ta fadi tana runtse idanunta sosai a cikin jikinta take jin wani iri zuciyarta na matsewa da wani irin yanayi da yake mikata wani mataki mai girman gaske. Dariya Baseera tayi cikin rashin baiwa batun muhimmanci sosai tana kallon Mariya da idanunwanta ke a rufe. "Ban gane ba Mariya me kike nufi kin san kuwa abin da kike cewa?". Buɗe idanunta tayi sosai wanda suka kaɗa sukayi jajir ganin hakan yasanya Baseera nutsuwa tana kallon ta lokaci guda zuciyarta ta buga da wani irin tsoro da ya mamaye duk ilahirin jikinta. Gyaɗa kai Mariya ta shiga yi kafun ta motsa laɓɓanta. "Ki taimaka ki auri Dr.Aqeel Baseera". Ta sake fadi tana kara kusanto Baseera fizge hannunta tayi gami da mikewa kallon Mariya take yi da wani irin yanayi kafun ta ja da baya sosai tana sake yi mata wani kallo mai kama da na tsoro ita kanta Mariya ta tsoro ta da irin kallon da take yi mata mikewa tayi tana takowa in da take ta sake riko hannunta tana sarkewa da nata. "Ki taimaka Baseera ki aure shi wannan hanyar ce kawai nake hango mana mafita a gareni da kowa ma". Kallonta take yi sake da baki kwanyarta take ji tana mikata wani mataki mai kokarin kona mata kwanya zuciyarta take ji tana harbawa da sauri-sauri. "Ki taimaka ki aure shi na san za ku dace kuma za ku so juna". "Ba zan iya ba Mariya ba za ayi wannan cin amanar dani ba". Ta fadi tana fizge hannayenta tana kokarin ficewa daga cikin dakin da sauri Mariya ta riko ta sosai ta juyo da ita idanuwanta suka kawo kwalla sosai cikin rawar murya Mariya ta fara magana. "Karki kawo cin amana a wannan lamarin Baseera ni nace na amince miki kuma na san ba haramun bane don haka don Allah ki anshi bukatata hakan ne zai tabbatar da amincin ƙawancenmu". "Ki yi hakuri ba zan iya ba Mariya". "Ki taimaka ki auri Dr.Aqeel Baseera ba za kiyi da na sani ba ni za ki taimakawa". "Mariya....!". Da sauri Mariya ta kai hannunta ta rufe mata baki tana girgiza kai hawaye na sauko mata saman fuska. "ko MATAR MIJINA kika zama Baseera ba zan taba da na sani ba domin na san halin ki kuma na san ba zaki taba abin da zai cutar dani ba Baseera matsayin yar'uwa kike a wajena kina da matsayi mai girma a gareni ki anshi bukatata ki daure karki ce dani a,a". Runtse idanu Baseera tayi tana jin zuciyarta na mikata wani mataki mai girman gaske gabadaya komai ya cunkushe mata ta rasa wani tunani ma zatayi ba ta taba zato ko tsammanin Mariya wannan bukatar zata nema a gareta ba in da ta san haka ce zata faru ba abin da zai kawo ta wannan gidan amma ina ALKALAMIN KADDARA ya zano mata rubutun da sai ta zo ta karance shi. 'Anya ba cin amana in ta yarda da batun Mariya anya hakan ya dace bata jin son Dr.Aqeel a ranta ba ta jin sun dace a tsakanin ita dashi to in ita ta yarda shi fa a yarda ta ga yana mayan son Mariya an ya kuwa zai dube ta da idanun kirki har ya anshe ta a matsayin matar aure gareshi ina! ba zata yarda taje in da ba a son ta ba ba za ta je in da ba za a ganta da mutunci da kima ba ba zata yarda ta shiga in da za a din ga yi mata kallon kamar dole akayi masa ba'. Nazarin da ta shiga yi da zuciyarta kenan cikin wani irin yanayi tsoro da fargaba na kara bayyana a gareta. 'Mariya ta cancanci komai fiye da haka za ta so ace sanadin ta ta samu farin ciki za ta so ace ta sanadin ta rayuwarta ta sauya ta dawo mai armashi amma ta ya ya hakan zata kasance bata tunanin auren Dr.Aqeel shine mafita'. Kamar Mariya ta san nazarin da take yi da zuciyarta dubanta tayi cikin kara narkar da murya da son biyan bukatar ta duk da tana jin wani iri a zuciyarta ta. "Ki daina shakka ko fargaba akan Dr.Aqeel Baseera zai so ki ba zai taba wufutar dake ba so zai yi miki mai an suna so zallar sa karki sake ki saka wa zuciyarki fargaba ko tsoro". Hannu ta saka tana dauke hawanyen fuskarta tana mai kokarin zaunar da Baseera amma ta kiya ta kwace kanta. "Gida zan tafi Mariya kaina ciwo yake yi don Allah rabu dani zan yi tunani". "Ban yarda ba Baseera ba zan yarda ki fice daga cikin gidan nan ba har sai kin ansa mani bukatata in kuwa har baki an sa ba to na tabbata amincin dake tsakaninmu ba kai ya kawo ba wallahi tallahi Baseera ko mijin da nake aure ki ka zo ki ka nuna kina so wallahi zan yarje miki ki zama MATAR MIJINA". Da mamaki Baseera ke dubanta fuskarta na sakin wani murmushi wanda yafi kuka ciwo sosai ta kamo hannun Mariya ta saka a nata. "ki daina kiran amincin dake tsakani na dake kina danganta shi da wannan lamarin ni nace miki ki bari nayi tunani ba yarda za ayi na ansa wannan batun lokaci daya Mariya ba sauki fa lamarin nan gareshi ba duba zakiyi da shi Dr.Aqeel ba shi yace yana so na ba ke yake so kina tunanin in ya ji batun nan zai yarda har ya dube ni da kima da mutunci ya anshe ni amatsayin da kike kokarin daura ni?". Murmushi ita ma tayi zuciyarta na kara matsewa. "Alkawari nayi miki zai so ki so da bai taba yi wa wata 'ya mace...". "Ya isa haka Mariya maganar ta isa haka ki daina danganta KALMAR SO a wannan bahagon tunanin naki mara tushe kece mace ta farko kuma ta karshe da Dr.Aqeel yayi wa son da ba zai sake yi ma wata mace ba a duniyar...". "Na karya taki Baseera a wannan matakin ni nace miki in har kika aminci da Dr.Aqeel sai yayi miki so fiye da wanda yayi mani a filin duniyar nan ki rubuta wannan ki ajje ni dai BURINA ki amince". Kanta ta dafe da take jin yana sara mata maganganun Mariya suna kokarin saka mata ciwon kai bata san yarda za tayi da ita ba amma Allah na gani zuciyarta na fargaba kan lamarin nan. "ki je ki samu yardarsa in har ya amince nima na amince". Tana gama fadin haka da sauri ta kwace kanta ta fice daga cikin dakin zuciyarta da kwanyarta sai hayaki suke yi kamar za su kama da wuta duniyar take ji tana juya mata kafafuwanta take ji suna kokarin zubda ita ga wani zafi da take ji tun daga kasan ruhinta har zuciyarta komai kallon sa take yi kamar a mafarki ba gaske ba laɓɓanta take turawa cikin baki tana cizawa gami da runtse idanuwa. Dafe kanta Mariya tayi gami da jan kafafuwanta da take jin su ita ma suna kokarin zubda ita kasa ga wani hayaniya da take ji a kwanyarta zuciyarta take ji tana harbawa da sauri-sauri idanuwanta a runtse ta isa bakin gadon ta zauna tana faman fadin. "Yaa Hayyu Yaa Kayyum". Numfashi take fiddawa a hankali zuciyarta na kara mikata wani mataki abin da tayi ne a yanzu take jin wani banbarakwai ji take yi kamar ba gaske ba ji take yi kamar cikin barcinta ne komai ke faruwa girgiza kai ta shiga yi kafun ta buɗe idanuwanta wanda suka gajiya da kaɗawa sosai zuwa ja murmushi ta saki gami da rufe fuskarta da tafukan hannayenta ta fada kan gadon ta baya. Tunanin ta yarda zata fuskanci Dr.Aqeel take yi ba ta san ta yarda zai dauki maganar ba in ta je masa da ita bata san duban da zai yi mata ba akan wannan maganar anya ba zai ce ta yaudare shi ba anya ba zai ce ta ci amanarsa ba anya ba zai ce tayi masa BUTULCI ba? Tunanin da take ta faman yi kenan zuciyarta kuma ta kasu kashi biyu bangare daya na bata kwarin gwuiwar tunkararsa dayan barin kuma yana tsoratar da ita yanayin da za su kwashe da Dr.Aqeel sosai ta ji ko ina na jikinta yana sanya kwanyarta na kara rikicewa da rigimar da zuciyarta ke hango mata za su kwasa da Dr.Aqeel a maganar nan ya kamata tayi wani tunani dole ne ta nemo hanyar da da zata samawar kanta mafita sannan ta samu cikar fatanta da burinta. ******* Kai kawo kawai take yi tsakiyar dakin gabadaya ta hargitse yarda ka san wacce ta kwato kanta daga gidan mahaukata hannayenta saman kai sai yamutsa sumar kan ta take yi lokaci-lokaci take tsayawa tana jan numfashi tun da ta dawo gida ta rasa gane kanta maganganun Mariya ne kawai ke yi mata safa da marwa gabadaya take jin kwanyarta na kamawa da wuta ga zuciyarta na ta faman kokarin fallewa da gudu daga kirjinta tashin hankalinta na daɗuwa ji take yi gabadaya duniyar na sauya mata ji take yi kamar ba ita ba. Saitin katon Mirrow da ke dakin ta isa ta tsaya tana kallon kanta ta cikinsa l fuskarta take shafawa tana runtse idanu gani take yi kamar ba ita ba gani take yi kamar wata Baseerar aka ajje aka dauke ta ainihin. 'Ta ya ya za ta so Dr.Aqeel bayan sun taba soyayya da ƙawarta aminiyarta ta kut-da-kut anya kuwa zata iya zuciyarta take ji kamar ba zata amince ba ji take yi kamar zaman kishi za su yi da Mariya ji take yi kamar in ta amince Mariya zata dauke a maciyar amana a gareta'. Zuciyarta ce take ta faman dauko mata wannan maganganun suna kara rikita mata lissafi kofar dakin da taji an taba ne ya sanyata saurin juyawa Yah Tareeq ne ya shigo ganin yanayin da take ya sanya shi saurin isowa gareta yana yi mata kallon tuhuma. "Me ke damun ki Sister?". Ya fadi yana kokarin riko hannunta da sauri ta ja da baya dafe da kai ta zauna bakin gado tana mai da numfashi harɗe hannaye yayi a kirjinsa yana dubanta cikin wani irin yanayi kafun ya isa kusa da ita ya zauna kan loka din kusa da gadon. "Tambayarki nake me ke damun ki kin yi mani shiru". "Yah Tareeq bana jin dadi ne don Allah ka yi shiru bana son surutu". Da mamaki ya dube ta ganin yanayin da take ciki ya tabbatar masa da gaskiyar abin da tace mikewa yayi yana kokarin fita har ya kai bakin kofa sai kuma ya tsaya gami da juyowa ya dube ta ita ma shi take duba dawowa yayi da baya hakan ya sanyata runtse idanu so take yi ya fita so take yi ta zauna ita kadai zaman kadaici take so kwanyarta take so ta sauke daga hayakin da take yi tana bukatar zaman ita kadai domin samun mafita akan wannan Bahagon lamarin da yake kokarin rikita mata lissafin rayuwa. Kusa da ita ya zo ya zauna bata ce dashi komai ba har zuwa lokacin idanuwanta a rufe suke tana faman jan numfashi da sauri-sauri. "Sister wai shin ya maganar nan ta mu ne har yanzu ba ki ce dani komai ba lokaci tafiya yake yi?". Duban sa tayi ta gefe idanuwanta a zazzare ji take yi kamar ta kwala ihu don haushin abin da yake cewa da ita so yake yi ya sake rikita mata lissafi bayan tashin hankalin da take ciki laɓɓanta ta tura cikin baki ta ciza da karfi har sai da ta dan saki kara ta dube shi sosai sai fama gyaɗa kai take yi. "Yah Tareeq ka san me nake so da kai?". Girgiza yayi cikin mutuwa jiki ganin yarda tayi masa maganar. "Ka taimawa kan ka ka taimaka min ka bar maganar nan don ba zata taba yuwu ba ne Yah Tareeq kayi hakuri ka je ka nemi wata matar amma ba Mariya ba don a halin da ake yanzu bana tunanin za ta iya dubanka har ta anshi tayin ka in har ba so kake yi abubuwa su lalace ba". Zaro idanu yayi waje sosai gami da mikewa cikin hanzari ya shiga kokarin magana amma Baseera ta dakatar dashi bayan ta mike idanuwanta sun kara kaɗawa sun yi jajir. "Don Allah na roke ka Yah Tareeq wallahi tallahi abi nan ba zai taba yuwuwa ba kawai bata lokacin mu za muyi sannan kuma kayi dakon son da ba zai yi maka amfani ba sai ma matsala da zai ja maka kawai kayi hakuri ka nemi wata ZABIN ALLAH shine kawai mafita". Tana gama fadin haka ta koma ragwaf! ta zauna dafe kansa yayi da yaji yana juya masa kamar zai zubda shi ya shiga ambaton Allah a hankali ya fara jin saukin zafin zuciyarsa kallon Baseera yayi yanayin da yake ganinta a ciki ya tabbatar masa da abin da take gaya masa da sauri yaja jiki yana hada hanya ya fice daga cikin dakin dagowa tayi ta dube shi bayan taji alamun ficewarsa ta girgiza kai ta koma ta kwanta.... *KAMALA MINNA*😘😘😘😘 [10/22, 5:24 PM] DEENY MINNA🙋‍♂:   UKU BALA'I NA. KAMALA MINNA. *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA SITTIN DA BIYU Gabanta take ji yana faduwa sosai da sosai ga wani irin yanayi da take jin gangar jikinta na shiga runtse idanu tayi a daidai lokacin da Umma ta shigo cikin dakin dauke da bokitin Cake da ta gama yi can gefe ta ajje shi sannan ta juyo ta dubi Mariya da tayi shiru kamar wacce ake yiwa wasiyya girgiza kai tayi kafun ta motsa laɓɓanta. "Kin ga Cake din nan na yau ya bani mamaki kamar ba yarda ake yi ba wallahi yayi albarka sosai". Ta fadi tana mai zaunawa gefe gudu har zuwa lokacin idanuwan Mariya na buɗe sai faman ajiyar numfashi take yi hannu ta kai saman kirjinta ta dafa gami da buɗe idanuwan nata tana duban Umma. Murmushin yak'e ta sakar mata kafun ta mike ta iso gareta jikinta a sanyaye. "Umma jikina nake ji wani iri wallahi ga kirjina sai bugawa yake yi kamar wani abu zai faru dani tun safe nake jin haka". Dubanta Umma tayi idanuwanta na yawatawa akanta so take yi ta hango wani abu da zai bata ko tabbacin abin da yake damun Mariyar. "Addu'a kawai zaki tayi Mariya irin haka in yana samun bawa musamman faduwa gaba Innalillahi wa inna ilaihir raji'un ake so ya ta maimaitawa". Gyaɗa kai tayi tana juyar da ganinta zuwa ga bokitin Cake din sannan ta juyo ta dubi Umma. "Yayi auki fa a hakan ma na gani...ko da yake Birin gidanmu ba ya nan shiyasa Cake din bai shiga uku ba". Mariya ta fadi tana murmushi ita ma Umma murmushi tayi don ta gano da Mu'azzam take.... Da gudu ya fado cikin dakin yana hak'i ya fada jikin Umma dukkan su suka dube shi da mamaki dago fuskarsa yayi ya dubi Umma sannan ya dubi Mariya. "Ga wasu mutane nan a kofar gida su hudu har da masu kayan fulani". Gaban Mariya ne ya yanke ya fadi kamar yarda yake yi mata tun dazu da sauri ta dubi Umma dafe da kirji yanayin ta ya sauya lokaci guda. Ita kanta Umma ta ji faduwar gaban sosai don sai da taji cikinta yayi kara zuciyarta na tsalle kamar zata fito waje. "Wai cewa yayi na zo na sanar daku nan gidan su ka zo daya daga cikin mutanan yace mani haka kuma yana kama da Yah Mariy....". Wata irin zabura Mariya tayi ta mike kan kafafuwanta idanuwanta a warwaje bugun zuciyarta take ji yana sauyawa sosai haka kawai take ji a jikinta akwai abin da ke faruwa. Umma kuwa rintse idanu tayi tana ambaton sunayen Allah da dukkan wata addu'a da ta zo mata baki haka kawai ta ji a jikinta akwai kamshin wani abu muhimmi a batun Mu'azzam. "Yace fa ku zo yanzu Umma". Ya fadi ya na mai jan hannun Mariya bayan ya tashi daga jikin Umma a hankali Mariya ta shiga bin sa kamar rakumi da ak'ala tana kallon Umma ita kanta Umma rasa abin yi tayi domin gabadaya take jin wata gajiya da kasala ta dirar mata a jiki lokaci guda ga wani bugu da zuciyarta take ta faman yi ba ƙanƙautawa laɓɓanta tashiga motsawa ta na son yi wa Mariya magana amma kamar an dora mata katon dutse a harshe hannunta tayi mata nuni dashi ta dauki mayafi . Duban jikinta tayi ita sam ta manta ma da kayan dake jikinta a hankali ta kwace kanta daga hannun Mu'azzam ta ja kafafuwanta da take jin su kamar za su zubda ita kasa ta janyo hijabin Umma ta zira ajikinta fita tayi cikin kokarin saita kanta Mu'azzam na gaba tana biye dashi har suka isa soron gidan nan ta ci burki ta tsaya jin yarda zuciyarta take dokawa da sauri-sauri jingina tayi da bango tana mai da numfashi Mu'azzam shi kam idanu ya zuba mata har ta gama shan sharafinta ta taka a hankali suka cigaba da tafiya har suka isa kofar gida sai dai me. Abin da Mariya ta gani ne ya kusan kashe ta da ranta runtse idanuwanta tayi sosai tana mai daura hannu aka ta kurma ihu gabadaya ta sulale zuwa kasa da sauri suka yo kanta ba wanda ya tabata ganin Babbar mace ce duban Mu'azzam sukayi gabadayan su kafun Baffa yace "Me ya same ta?". "Mu'azzam da yayi firi-firi da idanu cikin yanayi na tsorata. "Yah Mariya". Ya fadi ai Bello na jin haka ya sake dubanta sosai zuciyarsa da kwamyarsa suka mika shi wani mataki mai tsayin gaske da ya gama shuɗewa sosai yaji wani irin abu ya dokar masa zuciya mai girman gaske. 'Mariya'. Ya furta hakan a ransa yana sake muntsuka idanunsa yana saukewa akanta juyawa yayi da sauri ya fizgo gorar ruwan dake rataye a jikin Ja'e ya balle kanta ya shiga kwarara mata kamar yarda hawaye lokaci guda suka shiga zubo masa a fuska wani dogon numfashi ta ja gami da buɗe idanunta ganin mutanan dake kanta ya sanyata saurin runtse ido tana furta. "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un". Da karfi komai ganin sa take yi kamar ba gaske ba sosai zuciyarta ta tsorata ta sosai take jin jikinta wani iri gani take yi kamar a mafarki ba gaske ba laɓɓanta ta tura cikin bakinta tana cizawa zafin da yake ratsa ta ne ya tabbatar mata da GASKIYAR LAMARI da sauri ta sake ware idanunta. Fuskar dake saitin ta take kallo fuskar da take hango hawaye suna zuba a samanta fuskar da ta jima tana cigiya fuskar da ta bace mata a rayuwa tsayin shekaru wai ita ce yau take gani kunnuwanta ta rufe da tafukan hanayenta gami da sake runtse idanu zuciyarta na harbawa da wani irin yanayi wanda ba za ta ce ga matsayin da zata ajje shi ba. "Mariya". Muryar da ta shuɗe sama da shekaru bakwai ita ce yau take jinta a saitin ta tana ambatar sunanta muryar da tayi kewarta muryar da kullum take yabonta da shi mata albarka yau ita ce ta dawo gareta bayan shuɗewar lokaci. Wani irin kuka ne taji ya zo mata da saurin ta rufe bakinta amma ina sai da sautin sa ya fita da sauri ta shiga kokarin mikewa amma ina ta kasa gaɓɓanta take ji kamar an doke mata su kamar daga sama taji hannaye da tajima da saninsu sun riko mata kafaɗu cikin wani irin yanayi suna mikar da ita kan kafafuwanta wani numfashi take ja mai tafe da kuka buɗe idanuwanta tayi sa'ilin da taji ana dauke mata hawayen fuska sosai take kallon sa da wani irin yanayi na mamaki da tu'ajibi gani take yi kamar bashi ba gani take yi kamar gizo yake yi mata hannayenta ta shiga dagawa tana kokarin kai fuskarsa amma ta kasa da sauri ta shiga ja da baya tana duban sauran fuskokin wanda bata shaida su ba amma a jikinta take jin wani irin yanayi game da su. Da gudu tayi cikin gida kamar wacce za a sace a soro suka ci karo da Umma da Mu'azzam a hargitse domin tun lokacin da ya ga ta fadi din nan ya kwasa yayi cikin gida yana kiran Umma. Kallon ta Umma take yi da wani irin yanayi gabanta take ji yana yankewa yana faduwa hawayen da ta gani a fuskar Mariya ya kara rikita mata lissafi da sauri ta riko hannunta jikinta sai faman ɓari yake yi bakinta na karkarwa. "Su waye Mariya...tambayarki nake yi su waye?". Yanayin da take maganar kawai ya isa ya tabbatar maka da cewa sosai take cikin firgici Mariya da ta ga yanayin da Umma ke ciki ya sanyata sake rushewa da kuka kafun ta tsagaita da cewa. "Umma Allah yasa ba mafarki nake yi ba gaskiya ne Abbana ne...". Da sauri ta sake ta tana ja da baya gabanta na kara tsananta bugawa kafafuwanta take ji suna lauyewa idanuwanta suna lullubewa lokaci guda taji duniyar na juya mata kwanyarta na ansa kuwwa sosai jingina tayi da bango tana maida numfashi kafun ta zabura kamar wacce aka tsikara tayi hanyan waje da sauri a daidai lokacin shikuma ya sanyo kai cikin gida cikin rashin tsammani suka bangaji juna taga-taga Umma tayi zata fadi dama ba wani karfin jiki take dashi ba da sauri ya rikota gabadaya jikinsu ya dauki wani irin yanayi runtse idanu Umma tayi sosai tana jin yarda jikinta ke ansawa da wasu bakin lamari masu girman gaske gareta. A hankali ta shiga kokarin buɗe idanuwanta tana saukewa gareshi bakinta dauke da addu'a don gani take yi kamar a mafarki ba gaske ba jikinta na rawa ta dago hannunta tana shafe fuskarsa lokaci guda wasu hawaye suka shiga kwaranyo mata a fuska zuciyarta na kara matsewa kwanyarta take ji kamar za ta kama da wuta a hankali ta zare jikinta daga na shi tana ja da baya kallonsa take yi a yanzu cikin tuhuma shi kansa ya hango hakan da sauri ya dube ta amma ita juyawa tayi tana kokarin komawa cikin gida. "Tare da su Baffa nake". Da saurin Maganganun nasa suka bugar mata zuciya da kwanya lokaci guda jinin jikinta da numfashinta sukayi tsayawar wucin gadi ji tayi kamar ba a duniya take ba kunnuwanta sai faman maimaita maganar da Bello yayi suke wani GWAURON NUMFASHI taja da take jin kamar zai fasa mata kirji tsoro ne sosai ya bayyana a gareta maganar take ji kamar ba gaske ba so take yi ta gasgata zuciyarta take jin tana ansawa tana amanna da batun juyawa tayi cikin wani irin yanayi mai wuyar fassaruwa ta dube shi wani kuka mai girma taji yana zuwa mata zuciyarta na buɗe wani wawaken ciwo da ta jima tana jinyarsa. A hankali ya isa gareta yana riko hannayenta gami da girgiza kai idanuwanta sai faman bin shi da kallo suke komai take ji kamar almara gani take yi ko a cikin barcinta hakan ba zai faru ba amma zuciyarta sai kara karfafa mata guiwa take yi a kan ta yarda. Mariya da Mu'azzam suka iso garesu kallon kallo suka shiga yi a tsakaninsu Bello na duban su Mariya da Mu'azzam yana kuma duban Umma wacce ta zama wata butun butumi a tsaye zuciyarta take ji tana mikata wani mataki mai girma dauke da tashin hankali da ciwon rai ciwo ne mai girma zuciyarta ta fama mata shi wanda take ta jinyarsa ya kasa warkewa. Duban Mariya yayi yana son yin magana amma ya kasa wani irin yanayi yake jin kansa a ciki ji yake yi kamar ba shi ba. Sallamar da su Baffa sukayi ne ya sanya Umma mutuwar tsaye zuciyarta tayi wani bugun da sai da kirjinta ya daga da saurin ta runtse idanun tare da yin cikin gida da sauri sai faman hada hanye take yi. A daidai lokacin da suka shigo ta karasa shigewa cikin gidan don haka Bello yayi musu jagora suka karasa shiga sai bin gidan suke yi da kallo Baffa na faman gyaɗa kai zuciyarsa na matsewa da ciwon da yake ji yana motsa masa tsayin lokaci wai shine yau a garin Gwada garin da yayi wa kansa alkawarin ba zai taba WAIWAYE izuwa gareshi ba yau shine a ciki a kuma gidan da 'yarsa take aure wacce ita ce silar barin sa garin hawaye idanuwansa suka kawo da sauri ya shafe su ciki da nadamar abin da ya aikata wanda yake jin ya cuci kansa sannan ya cuci 'yarsa. Har cikin dakin su ka shiga zaune take ta hada kai da kafafuwanta zuciyarta na ta faman harbawa da wani tashin hankali mai girman gaske sallamar da taji Muryar Baffa na yi ne ya kara jefata tashin hankali runtse idanuwanta tayi gami da sake kankame kanta da sauri Mariya ta isa gareta ta zauna gefenta ganin halin da mahaifiyar tata take ciki ya sanya ta duban su Baffa da sukayi carko-carko a tsakar dakin lokaci guda kirjinta taji ya buga kallon Baffa ta shiga yi zuciyarta na dauko mata wani lamari da tunanin mai girma da take son ta tabbatar da gaskiya a kansa can kasar zuciyarta take furta 'Baffa' da sauri ta sake duban Umma sannan ta dubi Baffa zaro idanu tayi waje ta shiga nuna shi da yatsa laɓɓanta sai motsawa suke yi. "Umma dago kanki wannan kamar Baffanki?". Mariya ta fadi Muryarta na rawa sosai Baffa da ke tsaye a hankali ya tako ya iso garesu hannun Umma ya riko wanda taji rikon a bazata sosai ta firgita tare da kau da kanta domin bata son kallonsa ta san ita mai laifi ne laifin ta mai girma ne a gareshi. "HABEEBA!". Ta ji ya ambaci sunanta da muryar mai laushi wacce rabon da taji ta har ta manta dago kanta tayi wanda sukayi face-gace da hawaye ta sauke a fuskarsa murmushi ta ga yanayi mata hakan ba karamin mamaki ya bata ba bakin ta na rawa. "Baffa na san ni mai laifi ce ban cancanta ka dube ni ba ban cancan ci ka zo gareni ba Baffa na tuba na san na kuntata maka na san na dasa maka ciwo a zuciya shiyasa tun da na rabu da kai har yau ban samu natsuwa da kwanciyar hankali ba...". "Habeeba". Ya sake fadi da muryarsa mai taushi gami da nuna mata alamun tayi shiru hakan yayi matukar bata mamaki wai Baffanta ne haka yau shine yake yi mata magana a cikin salama ba zata taba manta ranar da ya rabu da ita ba ya mikata a hannun Bello yace ya yafeta amma yaushi ne a gareta abun yayi matukar daure mata kai sake runtse idanu tayi don ita har yanzu ba ta yarda wai Baffa da Bello bane a gabanta. "Habeeba ki daina fadin haka ni Mahaifinki ne nasan na dauki hakkinki na sanya ki cikin damuwa da rashin kwanciyar hankali a dalilin son zuciya irin tawa ina neman afuwanki ki yafe mani nima na yafe miki duk wani laifi da ki kayi mani ga mijin ki nan ya fada min komai". Wani kuka ne ya sake sarke ta shiga yin sa ba kankautawa ba wanda bai tausaya mata ba cikin dakin Ja'e da Iro su kan su sai da suka ji tausayin yayar ta su gwuiwowinta a kasa take neman afuwan Baffa Mariya da Mu'azzam suma haka suke yi suna taya ta rokon Baffa kamar yarda suka ga tana yi sai da suka shafe tsayin lokaci a haka kafun suka yi shiru nan dakin ya dau shiru. Baffa ya shiga karanta mata komai da ya faru da Bello don sam! Umma kamar ba tayi maraba dashi ba sosai yayi mata bayani sannan ta yarda shima ya kora mata da irin matsalolin da ya fuskata da irin SIRAƊIN RAYUWA da ya fada sosai Umma tayi kuka jin irin bala'in da mijinta ya fada ciki musamman da taji yace bai san lokacin da ya tafi ya bar su ba shi dai kawai ya tsincin kansa a wani waje ne. "Wai hayaniyar me nake ji ne cikin dakin nan tun dazu kamar gidan yan barik...". Guntse sauran maganar ta tayi daidai lokacin da ta daga labule idanuwanta suka sauka kan na Bello da ya kafe ta da idanu hannunsa rungume da Mu'azzam mutuwar tsaye tayi kafun ta dawo hayyacinta tana duban mutannan cikin dakin daya bayan daya idanuwa a warwaje kamar wacce tayi wa sarki karya bakinta ya fara motsi jikinta yana rawa ta shiga fadin. "Bello dama kana duniyar nan". Da sauri ya ansata da murmushi a fuskarsa. "Ga zahiri kin gani Goggo Marka". Da sauri ta juya tayi waje har tana tuntube dukansu suƙa hada idanusu kowa da abinda ke ransa... *KAMALA MINNA*😘😘😘😘😘  UKU BALA'I NA. KAMALA MINNA *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA SITTIN DA UKU. Hajiya Layla ce ta dubeshi a karo na ba adadi zuciyarta na mikata wani mataki na tausayi amma so take yi ta kwace kanta domin sam Dr.Erena ba abin tausayi bane ba abin ma a tsaya ana sauraron batutuwan da yake yi bane na rashin hanyyaci. sosai zuciyarta take kuna gami da suya kwanyarta take ji tana kokarin kamawa da wuta laɓɓanta ta shiga motsawa tana kokarin yin magana amma ta kasa sai ma wani tari da ya zo mata da sauri ta koma gefe nesa da inda Dr.Erena yake a kwance saman gadon asibiti yana ta faman numfarfashi gabadaya ya sauya daga kamanininsa yayi wani irin baki ga idanuwansa da sukayi jajir sunyo waje sosai bakinsa ya karkace ya koma ɓarin dama fuskarsa gabadaya duk ta mokaɗe. Tari take yi sosai wanda har sai da ya kaita zaunawa tana dafe da kirjinta hannu daya kuma ta rufe bakinta dashi sosai tarin take jinsa yana mata ciwo daga cikinta har zuwa kirjinta da take ji kamar zai fashe. Areefa dake zaune can gefe daya takure gabadaya ita kanta tayi zuru-zuru kamar wacce ta tashi daga amai da gudawa mikewa tayi da sauri gami da daukar gorar ruwa ta nufi wajanta gami da riko mata hannu sai dai me? Abin da ta gani ya sanyata saurin ja da baya tana duban hannun Hajiya Layla da ta cire daga bakinta sosai idanuwanta sukayo waje wani bakin abu ne mai kauri gami da yauk'i yake zubowa daga bakinta runtse idanu Areefa tayi sannan ta buɗe mikar da Hajiya Layla tayi ta kai ta Toilet ta wanke mata baki sannan suka fito. Gefe guda ta zauna tana ta faman mai da numfashi kamar wacce tayi gudun ceton rai. Sosai zuciyar Areefa ta karye sosai take jin wani irin abu nayi mata ciwo a zuciyarta tsoro na kara bayyana yanayin da take ganin Hajiya Layla a ciki ba karamin tashin hankali yake saka bata ba tun yau ba ta lura da ita tana cikin matsala amma take boye mata ko tayi mata magana su je asibiti a dubata cewa take yi a,a ta barshi akwai maganin da take sha a da can baya tana dadewa bata yi ba amma yanzu a wuni sai tayi tari yafi a lissafa. Motsin buɗe kofa ne ya katse mata tunanin zucin da take yi da sauri ta dubi kofar Alhaji Abdulwahaab ne ya shigo fuskarsa a tanke kamar ba a taba halittar fara'a fuskar ta shi ba duban su yayi su duka ganin yanayin da Hajiya Layla ke ciki ya sanya shi tsaida kallonsa a kanta. "Hajiya Layla ya ya dai na ganki cikin wannan yanayin?". Girgiza kai tayi ba tare da tace dashi komai ba can gefe yayi ya dauko Remote dake kan loka din gadon asibitin ya shiga Control din Tv bango da yake a kusurwar dakin na dama a can sama a hankali ya shiga canza tasha har ya zo kan tashar NSTV MINNA sannan ya tsaya yana mai maida hannayensa duka baya ya juyo ya dubesu suma shi suke duba bai ce musu komai ba har illa nuni da yayi musu su mai da hankalin su kan labaran da ake yi cikin harshen turanci. A hankali ka shiga labarai hankalin su na kai har aka zo in da ya kusan kashe su a zaune Areefa ce ta mike da sauri tana nuna Tv da dan yatsarta dake ta faman rawa Company din Dr.Erena na ne aka nuna yan kwana kwana na ta aikin kokarin kashe wutar da take ta faman ci akan sa kamar WUTAR DAJI sosai mutane suka cika wajan sai faman kallo ake yi yan kwanakwana na ta aikin su amma ina kamar kara rura wutar ake yi. Dr.Erena da yake cikin halin rashin hayyaci da yake Tv din na saitin sa idanuwansa na kan Tv din ganin abin da ake haskowa ya kara rikita masa jiki da sauri ya shiga mutsu-mutsu yana faman kakari yana kokarin daga yatsarsa amma ya kasa dukkan su duban sa suka shiga yi ba wanda ya motsa suka cigaba da kallon su ihun da yake kurmawa ne da wani irin kuka kamar na kare ya kara rikita dakin da sauri Alhaji Abdulwahaab ya kashe TV din tare da komawa gefe ya harɗe hannayensa yana duban su Areefa da hankalin su ya gama tashi. "Ajiya cikin dare Company ya kama da wuta ba tare da kowa ya sani ba tun misalin karfe biyu na dare a halin da ake yanzu duk masu gadin Company din sun mutu wajajen Asuba ne aka ankara da wutar nan aka sanar da yan kwana-kwana suka iso to dai har zuwa wannan lokacin ba suyi nasarar kashe wutar ba kuma sai kara ci take yi yanzu haka fitar da nayi can na nufa manaja din ne ya kira ni yake sanar dani abin da ke faruwa". Ya karashe cikin nuna halin-ko-in-kula yana duban Dr.Erena da ya gama ficewa daga hayyacinsa gabadaya ya muttsuke jikinsa yana ta faman kartar fuskarsa. Jinin da yake zuba a bakinsa ne bakinkirin ga hannayensa da ya saka ya shake wuyansa a hankali ya dinga ihu mai tsananin kara lokaci guda ya tiko kasa yana numfashi kirjinsa na faman dagawa lokaci guda kuma ya tsagaita ya daina motsi gabadaya. "Kun ga ku tashi mu bar asibitin nan tun kafin wahalar mutumin nan ta kashe mu ai mun yi masa na Allah tunda har muka kawo shi asibiti mukayi jinyarsa ta kwanaki". Ya fadi yana duban su kafin ya shiga toshe hancinsa wani irin warine yaji ya karaɗe dakin gabadaya da sauri ya juya ya fice ji yayi kan sa na juyawa Hajiya Layla ce ta dubi Areefa da tayi tsaye cikin tsananin tashin hankali ganin yarda Dr.Erena ya koma kamar bashi ba wani irin tsoro da fargaba suka shige ta ta daga hannu tana kokarin nuna shi da sauri Hajiya Layla ta riko mata hannu suka fice daga cikin dakin. Alhaji Abdulwahaab suka hango tafe da wani likita cikin hanzari ya iso garesu gami da duban su kafin yasaka kai cikin dakin runtse idanu yayi ganin yarda Dr.Erena suffar ta juye ta koma kamar ta kare a hankali ya taka hannunsa toshe da hancinsa jin warin da yake yi dubansa ya shiga yi kafun ya tabo wuyansa sannan ya shiga auna shi sosai ya tsorata ganin baya numfashi sake auna shi yayi domin tabbatar da abin da yake zargi mikewa yayi kan kafafuwansa. Yana kokarin fita ya ji wani kuka mai kama dana kare ya karaɗe dakin shi kansa sai da ya tsora ta da sauri ya juya ya dube shi gani yayi ya dawo hayyacinsa yana numfashi kusa dashi likitan ya karasa bakinsa ya gani yana motsi magana yake yi amma bata fita sai da yayi tari gami da watso wani bakin jini sannan sunan Areefa ya fito daga bakinsa yana faman nuna kofar waje jikinsa sai karkarwa yake yi juyawa likita yayi ya dubi kofar gami da mikewa ya fita can ya hango su har sun kusan barin bangaren kwala musu kira yayi gabadayan su suka juyo yayi musu nuni da hannu da su dawo. Ko kallon arzuki ba suyi masa ba sai da yayi musu magiya sannan Areefa da Hajiya Layla suka dawo jan su yayi cikin daki suna shiga suka tadda Dr.Erena magashiyan likita ne ya isa gareshi gami da dago hannunsa ya saki ya fadi ragwaf da dauri ya sake duba sa saidai ina tuni lokaci yayi. Numfashi ya ja mai karfi gami da mikewa kan kafafuwansa yana duban su gyaɗa kai ya shiga yi. "Allah yayi masa cikawa". Zaro idanu sukayi waje gabadayan su kafun Hajiya Layla ta dubi Dr.Erena wani irin yanayi ta ji ta a ciki zuciyarta na kara tsorata wata irin nadama da kaicon wannan rayuwar tayi sosai take jin zuciyarta na mikata wani mataki na tsoro wai yau Dr.Erena ne haka cikin wulakantaccen yanayi cikin yanayin da ko kallonsa ba za ayi ba batare da an kau da kai ba wai yau Dr.Erena na ne haka duniya kenan mai yayi duniya kenan wacce ba ma tabbata ba kuma ba aljanna ba. Da sauri ta dubi Areefa wacce jikinta ya gama yin sanyi sosai idanuwanta du cika da kwalla hannunta ta kama tana kokarin fidda su daga cikin dakin likitan ne ya tsaida su yana mai fadin. "Sai ku zo ku dauki gawar ko domin yi mata suttura". Ko ta kan sa ba su bi ma shima bai damu ba duk a nasa tunanin mutuwarce duk ta ruɗa su haka shimfiɗar gadon ya janyo ya lullube gawar gami da ficewa daga cikin dakin yana jan kofar. ****** Kwance take tayi ruf! da ciki tunanin duniya duk yabi ya dame ta gaɓadaya duniyar take ji ta tsana komai na cikinta ya daina burgeta zuciyarta sosai ta tsorata ba abin da take tunawa sai yarda ta ga Dr.Erena ya koma kamar bashi ba halittarsa gabadaya ta sauya kamar ba ta DAN'ADAM ba Company din sa take tunawa yarda taga yana ci da wuta tunda take a rayuwarta bata taba ganin harshen wuta na tashi kamar igiya ba sai ranar wuta har kore-kore take yi yarda taga ana watsa ruwa amma kamar ana kara rura wutar hakan yayi matukar daure mata kai. Dafa kafadar da ta ji anyi ne ya sanya ta saurin jan numfashi gami da dawowa hayyacinta mikewa tayi ta zauna tana duban fuskar Hajiya Layla da murmushin yak'e zama tayi bakin gadon itama tana dubanta cikin wani irin yanayi kafun ta ja numfashi ita ma. "KHAIRIYYA!". Ta fadi da wata kwantacciyar murya da sauri Areefa ta dubeta jin ta kira sunanta na asali. "Ya kamata ace kin ajje komai a gefe na sani batun Dr.Erena na ne ke damun ki ba wani abu ba kuma ya kamata ki ajje batun sa agefe shi ai duniyarsa ta kare". Gyaɗa kai Areefa tayi gami da goge kwallar da ta zubo masa. "Maama zuciyata nake jin wani iri wallahi babu dadi tsoro nake ji yanayin da na ganshi a ciki". "Khairiyya kenan ai duk wanda yace zai kauce hanyar Allah yana aikata abin da ransa ke so aiko ba zai taba ganin daidai a rayuwarsa ba kin ga dai Dr.Erena kin ga yarda rayuwarsa ta kare a duniyar nan baki daya kamar ba a taba yin mai sunansa ba kina dai ganin dukiyar da ya tara da kadarori amma ba su yi masa amfani ba kin ga kenan duniyar ma bakidayanta ba komai bane wajan Allah balle kuma bawa da yake a cikinta yake abin da ransa ke so". Gyaɗa kai Kawai take yi tana jin wani tsoro na kara ratsa mata zuciya da duk wani sashi na jikinta sosai ta firgita da yanayin wannan rayuwa a wannan duniyar. "in har son zuciya zai zama ado ga dan'adam to tabbas yana cikin gagarin rayuwa in har dan'adam zai daura wa kansa buri na son abun duniya to yana tare da tashin hankali". ta sake fadi tana riko hannayen Khairiyya idanuwanta na kawo kwalla. "Khairiyya ki yafe mani na san nayi miki laifi mai girman gaske a filin duniyarki ina da hannu dumu-dumu wajan fadawarki wannan bala'in da kika fuskarta ina mai rokon afuwarki a karo na ba a dadi Khairiyya nayi dana sanin mu'amala da Dr.Erena nayi nadama nayi kaico in da nasan wannan rayuwar zan zaba miki wallahi ba zan taba amincewa da bukatarsa ba...". Da sauri Khairiyya ta kai hannunta saitin bakinta tana rufewa. "A,a Maama ki daina fadin haka dama can tun fil'azal ALKALAMIN ƘADDARA ya rubuto min hakan sai ya faru a gareni ba laifin ki a ciki". Wani kuka ne ya kwacewa Hajiya Layla sake damke hannun Khairiyya tayi tana jin wani irin kauna da sonta na kara ratsa mata zuciya da dukkan gangar jikinta sosai take jin Khairiyya kamar ita ta haife ta. "Ban san iyaye na ba san nan na rayuwa cikin kazamar rayuwa gashi ni ba aure nayi ba bare na samu wata zuri'a da za su jibance ni ina cikin UKU BALA'I a rayuwa ta Khairiyya...". Da sauri ta sake rufe mata baki hawaye na wanke mata fuska itama. "Ki daina fadin haka Maama kina da dangi kina da zuri'a ni duk zan zame miki duk wadannan abubuwan da kika rasa a rayuwa ki dauke ni a matsayin 'Ya Maama ki rikeni har karshen rayuwa mu rayu tare cikin MARAICI da ALKALAMIN ƘADDARA ya zano mana a rayuwar nan tamu". Sosai ta rungumeta ta matse ta a jikinta wani kuka ne sukeyi gabadayan su mai taba zuciya da ruhi kuka suke yi gabadaya sun fice daga hayyacin su an rasa mai rarrashin dan'uwansa a tsakaninsu sai da sukayi mai isar su sannan Khairiyya ta kokarta tayi shiru tana rarrashin Hajiya Layla wacce kukan nata ya kasa tsagaitawa sai yinsa take yi mai hade da tari kamar ranta zai fita... *KAMALA MINNA*😘😘😘 [10/24, 9:23 AM] DEENY MINNA🙋‍♂:  UKU BALA'I NA. KAMALA MINNA. *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA SITTIN DA HUDU. Duban idanuwanta yake yi dauke da wani irin yanayi mai taba zuciyar masoya wanda suka tsumu cikin kugin soyayya da kaunar juna fuskarsa sai kara yalwatuwa take yi da murmushi mai girman gaske janye idanuwansa yayi lokaci guda yana mai da numfashi kafun ya motsa laɓɓansa. "Mariya kin yi shiru baki ce komai". Murmushi ita ma tayi gami da tura dan yatsanta guda cikin baki kafun ta shiga kokarin magana. "Duniyarnan a yanzu jin ta nake kamar ba wanda ya kai ni farinciki a cikinta". Cikin mamaki da tuhuma yake dubanta jin abin da tace dashi sosai yake ji a zuciyarsa wani iri yanayi musamman yarda ya ga ta saki jiki dashi yau rana daya tana dariya gami da murmushin da yake kokarin hallaka masa zuciya. "me ke faruwa ne Preety? da alamun zuciyoyi sun kusan barin kunci zuwa farinciki". Runtse idanu tayi gami da buɗe su sosai akan sa kafun ta juya ta kalli kofar gidansu. "Mahaifina ya dawo". Zare idanu yayi cikin mamaki da kuma al'ajabi bakin sa yake motsawa yana son yin magana amma ya kasa wani farinciki ya ke jin kansa a ciki a daidai wannan lokaci da bai taba tsammani ba lokaci guda yaji kamar an watsa shi cikin aljanna don farin cikin da sauri ya kara takowa zuwa gareta kamar zai hade jikinsa da nata da sauri ta ja baya da murmushi afuskarta. "Are you Seriuos?". Ya fadi yana mai tallaɓe haɓarsa sai faman zabga murmushi yake yi gyaɗa masa kai tayi da sauri ya juya yana kokarin tunkarar kofar gidan da sauri ta daga masa hannu tana mai sanya idanuwanta cikin nasa. "Me kenan kake kokarin yi?". "Oh God! don Allah ki bar ni naje na gan shi kin ji kuwa yarda zuciyata take farin ciki kin ji irin dadin da nake ji a wannan ranar sosai nake jina a wani mataki mai girma wanda na jima ban shige shi ba ZUCIYARMU DAYA ne ni dake abu daya muka zama dole na tayaki farinciki dole na nuna kauna ga yanayin da kike ciki ayanzu". Yana gama fadin haka ya riko hannayenta ya fara kokarin janta da sauri ta fizge tana dubansa lokaci guda ta daure fuska tamau kamar ba ita bace mai dariya da farinciki yanzu idanuwanta take amfani da su tana tura masa hukuncin kuskuren da yayi a yanzu abin da ta tsana abin da bata so shine yau yayi mata tana soron irin wannan yanayin sam bata so ko numfashi suna hadawa da ɗa namiji domin kuwa sosai ta tsorata dashi musamman ganin halin da Hafsat ta shiga A DALILIN ƊA NAMIJI duk da dai ita har da yardarta da amincewarta domin ba yarda za ayi namiji ya saka mace yin abu dole ba tare da amincewarta. Sosai ya gane yayi kuskure sosai yake jin kallon da take masa yana bula masa jiki yana yanke masa hukunci mai girma runtse idanu yayi ganin yarda fuskar tata ta sauya a lokaci guda. "Kiyi hakuri Mariya hakan ba halina bane ban yi da wata manufa ba dokin farincikin ki ne shi ya je fani a wannan matakin da na so aikata kuskure mafi girma a gareki". Kau da kanta tayi batare da ta ce dashi kala ba ta fara tafiya domin komawa cikin gida shi kansa ya tsorota sosai ganin yanayin da take ciki a hankali ya fara bin ta a baya tana jin ta kunsa amma tayi banza dashi domin kuwa sai ta nuna masa kuskurensa ko da kuwa ba da gangan yayi ba. Ko da suka isa cikin soro juyowa kawai tayi ta dubeshi ta dauke kanta hakan ya sanya shi saurin tsayawa sai faman ware idanu yake yi yana jin yarda zuciyarsa ke wani irin abu kamar zata faso kirji ta fito waje. Bai san gangancin da ya kai shi aikata haka ba bai san tsautsayi da ruɗun da ya shige shi ba har ya aikata haka ba yake kokarin yiwa kasan salalar tsiya ya manta rabon da ya ga bacin ran Mariya amma yau daya abi sa kuskuren sa yana kokarin yi wa kansa SAGEGEDUWA... Motsin da yaji ne ya sanya shi saurin dawowa hayyacinsa daga duniyar tunani Mu'azzam ya gani tsaye hannunsa dauke da babbar sallaya da sauri ya isa gareshi yana kamo hannusa gami da durkusawa gabansa yana kallon sa cikin idanuwansa da wani irin yanayi riko sosai yayi wa Mu'azzam har sai da ya fara mutsu-mutsun kwace kansa. "Dagaske Abba ya dawo?". Ya tambayeshi don ya rasa ma abin da zai ce dashi fuskarsa yake kallo kamar ta Mariya sak! Runtse idanu yayi kafun yaja wani dogon numfashi ganin yarda Mu'azzam ke kallon sa kamar a tsora ce. Sakin sa yayi gami da mikewa ya anshi Sallayar ya shimfida Mu'azzam ya juya yana kokarin komawa ciki ya riko shi gami da jan sa a jikinsa suka zauna kan sallayar. Sun dauki lokaci a haka Dr.Karami sai faman tambayarsa yake tun yana ɗari-ɗari dashi har ya saki jiki dashi yana bashi labarin abin da ya sani suna cikin haka sai ga Abban ya fito da sauri Dr.Karami ya shiga kokarin mikewa yana sauka daga kan Sallayar yana zubewa cikin girmamawa da ladabi da sauri Abba ya riko shi fuskarsa da murmushi a cikinta. "Haba Hisham meye kuma haka kake yi sai kace wani karamin yaro tashi ka koma ka zauna". Ya fadi yana mika masa hannu suyi musabaha amma Dr.Karami sai wani nokewa yake yi yana mai jawo Mu'azzam yana zaunar dashi kan cinyarsa. Soron ne ya dau shiru na yan dakikai kafun Dr.Karami ya kara kasa da kai cikin murya kasa-kasa ya shiga yi masa jaje akan abin da ya faru. "Bakomai Hisham komai da ka ga ya faru a duniyar nan to dama tun fil'azal Allah ya rubuto shi a KUNDIN ƘADDARARMU". Ya nisa gami da sake duban Dr.Karami sosai, da kansa ke kasa wata kunya ce yaji ta lullube shi tun da yake bai taba yin haka ba yau ce rana ta farko duk sai ya jishi wani banbarakwai. "Ban san da bakin da zance da kai komai ba, ban san da wasu irin kalamai zan yi maka godiya ba, Hisham kayi mani komai a rayuwa kayi mani abin da ko dangina da yan'uwana bana tunanin akwai wanda zai iya hakan. Sosai naji dadi sosai naji farin ciki zuciyata ta jima tana kuna da takaici acan cikin wahalar da na tsinci kai na ban damu da tawa rayuwar ba sai ta IYALINA sosai nayi kuka nayi bakin ciki akan rashin basu kariya a ga rayuwarsu musamman a yarda na bar su na shiga tashin hankali tashin hankali mai girman gaske na tsani kai na tsani rayuwar da nayi dalilin ban san halin da IYALINA suke ciki ba...". "Abba da ka daina TUNA BAYA abin da ya wuce ya rigaya ya wuce kuma komai ya faru damu a duniyar nan ALKALAMIN ƘADDARA ne sila ba a son ranka komai ya faru ba ba wai kayi haka bane da wata manufa Allah ya ƙaddara sai ka je wani wajan ka rayu akwai abin da Allah ya gani ya sanya ya turaka wata duniyar kayi rayuwa". Dr.Karami ya fadi muryarsa can kasa sai faman wasa yake yi da yatsun hannun Mu'azzam. Hawaye Abba ya goge wanda bai san sun zubo masa ba sai da ya ji dumin su a hankali ya shiga baiwa Dr.Karami labarin rayuwar da ya tsinci kan sa har izuwa haduwarsu da Baffa... Sosai ya ji zuciyarsa wani iri sosai yaji tausayin su Mariya ya kamashi dago kai yayi ya dubi Abba da idanuwansa ke ta faman ZUBAR KWALLA zuciyarsa yaji tana kara matsewa da kaunar ahalin nan masu ciki da SADAUKARWA da kaunar juna su musamman yarda yaji AKAN SO suka fada wannan rayuwar su dukan su ashe haka akewa SO BIYAYYA ashe haka ake sadauƙar da komai da kowa a rungumi masoyi ashe shi bai ma yi so ba. Numfashi yaja mai karfi yana sake duban Abba wanda ya shafe fuskarsa kamar bai yi kukan ba sosai yake duban Dr.Karami yana jin wata kaunarsa na ratsa masa zuciya sosai yake jin zai iya yarda ya zama mijin 'yarsa domin ya yi amanna dashi da kuma irin nagartarsa ya tabbata 'yarsa ba zata koka ba a gidan sa so yake yi yayi masa magana amma ya kasa so yake yi yaji daga bakin sa in har ya furta KALMAR SO ga Mariya shi kuwa zai masa tukuici da ita. A hankali Dr.Karami ya shiga kokarin tashi alamun tafiya sallama sukayi ya mike har zuwa lokacin Mu'azzam na like dashi hannu ya saka ya zaro kudi masu dan dama ya ajje kan sallayar ya juya yana kokarin tafiya. "HISHAM!". Yaji Abba da wata irin muryar mai girma da zurfi a jikinsa yake ji kamar akwai abin da yayi ba daidai ba da sauri ya juyo ya dubi Abba kallon da ya ga yanayi masa yayi matukar bugar masa da zuciya sai dai murmushin da ya gani kuma ya bashi mamaki. "Zo ka dauki kudin ka don Allah". Ya fadi shima yana mikewa yana kara faɗaɗa murmushin sa, kuri yayi masa da idanu wani irin kwarjini ya ga yanayi masa magana yake so yayi amma ya kasa a hankali ya ja kafafuwansa ya iso gami da sanya hannu ya dauki kuɗaɗen. "Abba kayi Hakuri...". "Bakomai Hisham hidimar za tayi yawa ka gaishe da Hajiyar taka". Ya fadi yana mai juyawa ya koma cikin gida cike da farin ciki da kwanciyar hankali yarda yaga halayen Dr.Karami dama tuni Umma duk ta karance masa komai da komai da yake faruwa. Dr.Karami hannusa rike da na Mu'azzam suka isa bakin motarsa ya buɗe wata katuwar leda ya dauko ya mika masa kafun ya sake dauko wata ya bashi. "Wannan taka ce kai kadai ko Yah Mariya karka baiwa wannan kuma Umma za ka kaiwa". Dariya yayi gami da fadin 'Nagode' sannan ya juya ya fara tafiya yana daga masa hannu shima hannu yake daga masa yana jin kaunar wannan Iyalin na kara ratsa masa zuciya da ruhinsa.. ***** Da mamaki yake dubanta zuciyarsa na yayyagewa da tashin hankali bai taba zaton abin da zata fada masa ba kenan bai taba zaton in ya zo abin da zai tadda ba kenan in da yasan wannan bakar maganar zai tadda da bai zo ba zuciyarsa kara matsewa take yi da tashin hankali idanuwansa sun kaɗa sun yi ja duk wani farinciki da ya jima yana yi tun da yaji ta sanar dashi dawowar mahaifinta har rawar jiki yake yi wajan zuwa taya ta murna sai dai ashe ba nan gizo ke sakar ba. numfashi yake ja wanda yake jin sa kamar zai tafi masa da ransa duban ta yasake yi karo ba adadi kanta akasa yake yana hango yarda hawaye ke zubowa saman kuncin ta wani irim rauni ya sake jin zuciyarsa tana kara mikashi a ciki, hannayensa duk biyu ya dafe kansa dashi da yake jin yana faman kumbura kamar zai tarwatse laɓɓasa ya tura cikin bakin sa yana cizawa. "Mariya dama bakya so na dama duk BIYAYYAR SO da nake yi akan ki ta banza ce ashe akwai ranar da zaki nuna min iyakata haba! Mariya don Allah karki ce dani wannan maganar gaskiya ce don Allah ki ce wasa kike yi". Ya fadi yana jin duniyar na kara yamutse masa da wani irin tashin hankali mai girman gaske dago idanuwanta tayi wanda suka kaɗa sukayi jajir bakin ta sai rawa yake yi hannayenta dafe da kirjnta da take ji kamar zai tarwatse ita kanta ta san tayi ganganci ba ta san abin da yasa ta aikata hakan ba abin da take gudu kenan nayin BUTULCI ga Dr.Aqeel ta san batayi masa adalci ba batayi wa ita kanta adalci ba numfashi ta ja kafun ta sake dubansa sosai. "Kayi hakuri Dr.Aqeel ban yi haka don na tsane ka ba hasali ma ni ce mai son ka da kaunar k...". "Ya isa haka ki daina yiwa so karya akai na kawai ki fito fili kice bani kike so ba wani na kike so". Runtse idanu tayi tana jin sautin muryarsa mai sauti tana dukan zuciyarta da kwanyarta wani kuka ne ya kwace mata da sauri ta rufe bakinta jikinta ya shiga rawa numfashinta ya shiga tsittsinkewa hakan da Dr.Aqeel ya gani ya kara rikita shi da sauri ya iso gareta ji yake yi kamar ya rikota ya hadata da jikinsa ya rarrashe ta. "Kayi hakuri na san ban kyauta maka ba na san naci amanar soyayyarmu amma ina so ka dube ni da idon basira sannan ka fahimce ni ban yi haka don in tozarta ka ba ban yi haka don ba na son ka ba in da bana son ka ba yarda za ayi har nake tsayuwa da kai in da bana son ka ba yarda za ayi na bar zuciyata ta kauna ce ka ka sani ni da Baseera abu daya ne duk wani abu da kake tsammanin zaka samu gareni na kulawa da biyayya a soyayarka zaka samu a gareta fiye ma da haka hasali ma Baseera tafi ni komai da komai na rayuwa ina rokonka don Allah don Annabi ka dauki Baseera kamar yarda kake dauka ta ka sannan ina so kayi mata so kamar yarda kake yi mani koma fiye da hakan don Allah na roke ka in har son da kake yi mani kana so na kara gasgata shi to ina so ka komar dashi kanta". Ta fadi cikin rawar murya a hankali ta shiga ja da baya idanuwanta na kara ballewa da hawaye hannu ta daga masa kafun ta juya cikin sauri ta fada cikin gida. Runtse idanu yayi maganganunta yake ji suna yi masa yawo akai zuciyarsa yake ji tana kara matsewa da kalamanta da sauri ya ja jiki kafafuwansa yake ji suna harɗewa kamar za su zubda shi kasa ya fada cikin motarsa tare da yi mata key ya fizgeta ya fice daga cikin unguwar zuciyarsa na wani irin mataki wanda ba zai ce gashi ba... *Kamala Minna*😘😘😘 [10/25, 9:41 AM] DEENY MINNA🙋‍♂:  UKU BALA'I NA. KAMALA MINNA. *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA SITTIN DA BIYAR Sosai ya kasa gane kansa komai yake jinsa yana sauya masa lokaci guda zuciyarsa yake ji tana harbawa da wani irin yanayi mai raɗaɗi a zuciya bai san yarda zai yi ba bai san abin da ya kamata yayi ba zuciyarsa ta cushe kwanyarsa sai hayaki take yi kamar zata kama da wuta duniyar gabadaya yake ji tana kai komo dashi jin sa yake kamar bashi ba kamar wani daban aka dauko aka ajje. Numfashi yasake ja karo na ba a dadi yau kusan kwana uku kenan yana jinyar kansa kokari yake yi ya saita kansa amma hakan ya gagara zuciyarsa taki amanna akan abin da ake so yayi sosai yake jin GURBIN SO mai girma wanda ya baiwa Mariya ba zai iya barinsa ya so wata daban ba baya tunanin hakan zai iya kasantuwa son Mariya ta zama komai nashi ita ce rayuwarsa dama numfashin sa baya tunanin rayuwarsa zata yi karko in har ba soyayyar Mariya bace tadawo gareshi sosai yake kallon kansa a matsayin GAWA DA RAI. Hannayensa duka biyu ya dafe kansa da su yana faman jan numfashi mikewa yayi kan gadon yayi zaman dirshan gami da zabga tagumi yawatawa ya shiga yi da idanuwansa komai gani yake yi yana sauya masa komai yake ganin baya burgesa a filin duniyar nan komai yake ji kamar ciwo ne a gareshi zuciyarsa yake ji tana matsewa da wani irin tashin hankali mai girman gaske ji yake yi ko wani sashi da lungu na zuciyarsa na kara yayyagewa da son Mariya kokari yake yi ko zai iya abun da ta bukata amma ji yake yi kamar kara rura wutar sonta ake yi a zuciyarsa. A hankali ya zuro kafafuwansa zuwa kasa ya mike akan su jikinsa sanye da kayan barci farare masu dingo blue maballin gaban rigar ya gyara da ya fice ya zura silifas din dake yashe a kasa toilet ya nufa cikin rashin kwarin jiki da na zuciya. Yana shiga ya sakarwa kansa shawa mai ruwan dumi sosai yake jin ruwan na ratse shi ta ko ina zuciyarsa dake zafi yake jin tana sauka kadan-kadan runtse idanuwansa yayi yana furta. "Yaa Hayyu Yaa Kayyum". Kusan minti ashirin ya shafe a toilet din kafun ya wanke bakinsa gami da dauro tawul a kugunsa da wani kuma a hannunsa yana tsane kansa da sajen fuskarsa da yake karawa fuskart asa kyau da kwarjini fitowa yayi ya tsaya gaban Mirrow yana kallon kansa sosai yake hango ramar da yayi shi kadai ya san wahalar da yake sha shi kadai ya san azabar da zuciyarsa take kawo masa gabadaya ya daina jin dadin komai WALWALAR ZUCIYA gabadaya yanzu bai samunta har ya manta yaushe rabonsa ya jidadi da nishadi a duniyarsa. Numfashi ya ja gami da juyawa ya nufi sif din dake manne da bangon dakin buɗewa yayi yana kallon ko wani sashi na cikin sa kaya ne makil a cikinsa a shirye hannu ya sa ya shiga dagawa yana kallo so yake yi ya zabi wanda zai saka amma gabadaya kayan ma jin su yake yi wani iri ya jima a tsaye yana zarowa yana mai dawa ya rasa wanda zai dauko lokaci kankani duk ya yamotse sif din kafin ya zaro wani lallausar yaɗi light-blue mai dikon dark anyi masa dinkin zamani wanda ya fita sosai. Bakin gado ya ajje su sannan ya juya ya koma wajan Mirrow din fuskarsa ya dan gyara sannan ya koma ya zura kayan a jikinsa wanda sukayi matukar hawan sa sosai suka kara fidda masa da kyansa gami da kwarji agogon Rolex ya daura a hannunsa gami da kafa hularsa wacce ta hau kayan sosai takalmin kafarsa sau ciki baki sai daukar idanu yake yi glass ya saka a idanuwansa wanda ya kara sirrinta yanayin da yake ciki. Key din motarsa ya dauka gami da wayoyin sa bayan ya feshe jikinsa da daɗaɗar turarurruka masu sanyin kamshi a hankali ya shiga taka kafafuwanta yanayin sa kadai zai nuna maka ba ya cikin nishadin zuciya saidai cikar halintarsa da mazatakarsa da ka kalla zaka gane namiji hadadde mai ansa sunan sa na mijin. Kokari yake yi ya aikata abin da zuciyarsa take hana shi so yake yi ya koyi wannan rayuwar da aka zaɓar masa bashi ya zaɓa ba so yake yi ya koyi rayuwar da ake cewa ba zai yi nadama akan ta ba so yake yi ya matse zuciyarsa ta koyi abin da ake so ta koya so yake yi a wannan ranar komai ya canza so yake yi zuciyarsa da koyi kaunar wacce ake so ya mikawa soyayayarsa ya sani SO ƘADDARAR ZUCIYA ne so ne kadai ke wahalar da ita ya sata cikin duk wani kunci da gangar jiki zai wahala shi ma. Da wannan tunanin ya isa gaban sabuwar motarsa kirar Benz mai kalar baki sai faman daukar idanu take yi sai da ya kare mata kallo yau ne rana ta biyu da zai hau ta tun da yayo odarta haka kawai yaji yana bukatar ya fita da ita daga can nesa ya hango mai gadin sa hannu ya daga masa da gudu ya iso gareshi yana mai kwasar gaisuwa kafun ya mike ya nufi wajan Get ya hangame shi a daidai lokacin shi kuma Dr.Aqeel ya shige motar har yayi mata key ya doshi Get din a hankali har ya fice mai gadi nayi masa a dawo lafiya sannan ya mai da Get din ya rufe. **** Gabanta ne ya yanke ya fadi sallamar da tayi ba ta karasa ta ba taja burki ta tsaya sai faman rarraba idanu take yi shi kuwa ya kafe ta da idanu kamar zai haɗiyeta hakan ya kara rikita mata lissafi ji tayi kamar ta juya ta falle da gudu amma jin muryar Hajiya ya sanyataa motsa kafafuwanta da take jin su kamar za su zubda ita kasa a hankali ta shiga takawa tana karasa cikin falon ko ina na jikinta rawa kawai yake yi ga wani dokawa da gabanta ke yi musamman irin kallon da ta ga Tareeq na yi mata kau da kai tayi shiyasa sam bata son zuwa gidan nan ko don saboda shi ba ta son irin abin da yake yi mata. "Ina yini Mami". Mariya ta fadi bayan ta isa gareta ta zauna. "Lafiya lau Mariya ya gida ya su Umman taki da Abban naki?". Gyaɗa kai tayi kafun ta ansa da cewa. "Lafiya lau duk suna gaishe ku". Daga nan bata sake tsinkawa ba sai Mami ce ta sake cewa. "Shekaran jiya ai mun je kina Islamiyya ba mu tadda ki ba". Murmushi tayi gami da kokarin mikewa. "Umma ta gaya min Mami Allah ya saka da alheri ya kara buɗe gami da rufin asiri...". "Mariya kar ki sake kin ji ko ai mun zama daya komai aka yi muku a gidan nan ai ba faduwa bane kun zama yan uwanmu mu ma haka duk an zama abu daya...mutuniyar taki tana ciki kisan dai san halinta kullum tana kunshe a daki kamar mai zaman takaba". Dariya ta sake yi sannan cikin hanzari ta nufi sama sashin Baseera zaune ta same ta hannunta rike da littafi da sauri ta karasa kusa da ita ta zauna sam hankalinta ba ya jikinta domin tunani take yi ba wai karatun littafin ba da sauri Mariya ta zungurar mata kafaɗa a firgice ta dube ta ganin Mariya ya sanyata zaro idanu waje tana mai da numfashi ta shiga motsa laɓɓanta tana son yin magana amma ta kasa. "Kin kyauta Baseera wato shi ne kika dauke mani kafa ko kirana ma da kike yi a wayar Umma kin daina sabida na yi miki laifi mai girma ko har da ya kai kiyi mani hukunci irin haka....Hmm Hakuri na zo na baki akan abin da nayi miki ba daidai...". Da sauri Baseera ta rufe mata baki wasu kwalla na taruwa a idanunta ta shiga girgiza kai . "Ba haka bane wallahi ba na jindadi ne...". Turo kofar da akayi ne ya sanya Baseera saurin yin shiru tana goge fuskarta Mami ce ta shigo duban su tayi ganin yanayin da suke ciki batare da tace komai ba sosai suka gane kallon zargin wani abu take yi musu. "Baseera kin yi bako". Abin da ta fadi kenan ta fice daga cikin dakin gaban Baseera ya buga gami da duban Mariya da ita ma idanuwanta suke kanta kallan kallo suke yi wa juna kafun Mariya tayi murmushi tana mai dafa kafaɗarta. "Kin yi bako aka ce". Runtse idanu Baseera tayi tana jin yarda gabanta ke yankewa ya na faduwa. "Ban san waye ba Mariya ba muyi da wani zai zo waje na...". Daga mata hannu tayi tare da mikewa tana kamo kafarta doguwar riga ce a jikinta don haka ta janyo mata gyalan rigar ta yafa mata fuskarta ba wata baci tayi ba don haka ta ja hannunta suka fice. A harabar gidan suka hango mota girke da sauri suka dubi juna gaban Mariya ne ya fadi tana tunano inda ta san motar nan sosai ta ke ji a ranta ta taba ganinta amma ta rasa waye mai ita... Bata gama tunanin tuno mai motar ba ta ga an buɗe kofar ana kokarin fitowa da sauri ta runtse idanu jin yarda kirjinta ya doka rikon da taji Baseera tayi mata ne jikinta na karkarwa tana jin yarda take kokarin yi mata magana amma ta kasa hakan ya tabbatar mata da zarginta da sauri ta zare hannunta daga na Baseera tana kokarin juyawa ta koma ciki amma jin amon muryar sa ya sanyata tsayawa cak! tana mai da numfashi takun takalminsa da yake tunkaro su hakan ya kara rikita mata lissafi ta kara danke idanuwanta kamshin turarensa take ji ya dokar mata hanci zuciyarta take ji tana matsewa da wani irin yanayi tana mikata wani mataki bata san ya za tayi ba bata san da wani idanu zata kalle shi ba sosai take jin rashin adalcin da tayi masa a ranta haka kawai take jin wata kunyarsa ta ratsa ta. "Gani na zo domin yiwa so biyayya Mariya abin da kika bukata shi na zo yi domin tabbatar da abin da kike tsammanin ba haka bane". Wata irin bugawa taji zuciyarta tayi da sauri ta juyo gami da buɗe idanuwanta da suka kaɗa sosai ta dubi Baseera da tayi fakare da idanu tana dubansu daya bayan daya zuciyarta na bugawa da tashin hankali ashe da gaske Mariya take ashe abinda take faɗi mata zatayi ashe zata yi din da gaske. girgiza kai ta shiga yi tana saka idanuwanta cikin na Mariya da ta gama shiga wani yanayi mai wuyar fassaruwa. "Ban gane ba Mariya mai hakan ke nufi?". "Soyayyarta ta sadaukar gareki". Zare idanu Baseera fuskarta da wani irin yanayi mai girma a zuciyarta sosai take jin zuciyarta na matsewa da tashin hankali maganganun Dr.Aqeel take jin su wani iri a gareta sosai take jin suna hawa mata kai hannunta taji Mariya ta kama ta damke sosai da sauri ta dago ta dube ta idanuwanta ta gani cike da hawaye suna kokarim zuba. "Kin yi mani alkawari in har ya amince ke ma zaki amince don Allah karki watsa min kasa a idanu Baseera ki dubi Dr.Aqeel a matsayin masoyi mai kaunarki tsakani da Allah kiyi mani wannan sadaukarwar don Allah ban taba neman alfarma gareki ba sai yau don Allah ki anshe ta". Fizge hannunta Baseera tayi tana mai da numfashi zuciyarta take ji tana bugawa da wani irin yanayi. "A,a Mariya ba na tunanin hakan za ta faru karki takurawa zuciyoyin da ba sa kaunar junansu karki yi kokarin hada abin da kika san ba zai taba faruwa ba karki hada abin da kika san zuciyoyi ba za su samu farin ciki ba". Ta fadi muryarta na rawa wasu hawaye na zubo mata a hankali ta shiga ja da baya tana girgiza kai. A daidai lokacin shi kuma Dr.Aqeel ya kara takowa kusa da su sosai zuciyarsa yake ji tana matsewa da kuna gami da radadi runtse idanu yayi kafun ya buɗe su akan Mariya wacce gabadaya ta gama shiga wani yanayi idanu suka hada tayi saurin dauke nata zuciyarta na harbawa da sauri-sauri. "BASEERA!". muryar Dr.Aqeel ta doki kunnuwanta sautin na ansawa a kwanyar zuciyarta na buɗewa sosai tsayawa tayi cak! tana mai da numfashi kafun ta dube shi kallonta yake yi da wani irin yanayi wanda ba zata ce ga matsayin da zata ajje shi ba. "Na anshi soyayarki in har zaki iya bani nima zan baki zuciyata gabadayanta". Ya fadi yana mai runtse idanuwansa zuciyarsa yake ji tana matsewa da wani irin yanayi mai kokarin haifar da bugun zuciyar sosai yake jin idanuwansa na zafi da raɗaɗi ko ina na jikinsa yake jin lokaci guda ya tsaya jinin jikinsa yake ji ya shiga gudu da sauri-sauri kwanyarsa yake ji tana hayaki kamar zata kama da wuta. Mariya kuwa mutuwar tsaye tayi ba abin da take fadi sai 'Innalillahi wa inna ilaihir raji'un' wata katangar tashin hankali ne taji ta rikito mata hannayensa duk biyun ta saka ta dafe kirjinta da take jin yana barazanar tarwatsewa kanta taji ya shiga dokawa kamar zai rabe biyu muryar Dr.Aqeel da taji yana furta kalaman so jin saukar su take kamar garwashi wuta runtse idanu tayi gami da kokarin saita kanta kafun ta taka kafafuwanta da take jin su kamar za su watsar da ita kasa hannayenta ta kamo ta sarke a cikin nata. Idanuwansu suka sarke da juna murmushi Mariya tayi mai tafe da hawaye. "Ki amince ke ma Baseera zuciyoyinku su kasance waje daya su rayu tare su zama abu daya har gaban abada". Girgiza kai Baseera ta shiga yi idanuwanta na kara ballewa da hawaye a hankali ta zare hannayenta gami da duban inda Dr.Aqeel yake wani kallo tayi masa kafun ta juya cikin hanzari tayi cikin gida. Mai da numfashi Mariya tayi tare da duban Dr.Aqeel shima ita yake kallo kafun ya girgiza kai yana cizon laɓɓa wani murmushi yayi tare da juyawa ya nufi motarsa... *Kamala Minna*💞💞💞💞 [10/25, 5:38 PM] DEENY MINNA🙋‍♂:   UKU BALA'I NA. KAMALA MINNA. *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA NA SITTIN DA SHIDA A hankali take tafiya kanta akasa ga wani zundumemen Hijabi da ta saka a jikinta har yana sharar kasa hannayenta cikin hijabin sai wasa da su take yi. Kallo daya zaka yi mata ka gano yanayin rashin kwanciyar hankali a tattare da ita fuskarta tayi fari sosai ga wata rama da ta zabga kamar wacce tayi ciwon shekara guda. Ratso layin take yi tana bin gefe mutane sai binta da kallo suke yi kamar sun ga watan ramadana sosai take jin zuciyarta na zafi da raɗaɗin wannan fitowar da tayi bata taba zaton zata tsani kanta ba sai a cikin wannan kwanakin da fita ma gagararta take yi in kuwa ta fito an dinga zundenta kenan ana nuna ta da baki wasu har tararta suke suna gaya mata magana son ransu sai dai ba yarda zatayi ita ta jawo wa kanta. Cikin wannan yanayin ba zato ba tsammani taji an janyo mata hijabi ta baya wata irin dokawa taji gabanta yayi zuciyarta harba da sauri ta dago kanta cikin wani irin yanayi na tsoro da firgici dubansa take yi tun daga kasa har sama bata san shi ba bata san daga ina yake ba. "Ke ba kya ganin mutane ana yi maki magana kin yi banza da mutane iye wacece ke dan kan...". Ya lailayo ashar ya dire gami da daga hannunsa daya yana kokari kife ta da mari mai ya gani kuma sai ya sauke yana mai da numfashi. Sosai tsoro ya bayyana a fuskarta a hankali ta shiga ja da baya tana raɓashi zata wuce don ta lura dan iskan gari ne dan kwaya in ba don haka ba ai bai isa yayi mata wannan cin mutuncin ba ta kyaleshi da sai ta keta masa rashin mutunci amma halin da take yanzu ba zata iya ba duk da zafi da raɗaɗin da zuciyarta ke yi akan zagin kare dangin da yayi mata. Sake fizgo mata hijabin yayi ganin tana kokarin raɓashi ta wuce ya tsaya dab da ita har suna shakar numfashin juna ba abin da ke tashi a jikinsa sai warin solisho da sukuɗaye kau da kai tayi da sauri gami da toshe hanci wani yinkuri taji zuciyarta ta nayi tana kokarin yin amai. Ganin abin da take yi masa yasanya shi duban fuskarta da take yatsine masa tana toshe hanci wata irin ashariya ya danna mata gami da cafko hijabin jikinta ya cikuikuye. "Ke dan kan uban ki ni kike toshewa hanci to ubanki ne ke wari ba ni ba matsiyaciya karuwan banza da wofi". Yana fadin haka ya fizge hibajin gabadaya daga jikinta daga ita sai zani da ves ga katon cikinta da ya fito sosai wanda haihuwarsa nan kurkusa runtse idanu tayi gami da toshe kunnuwanta wani kuka ne ya zo mata da sauri ta durkushe tana mai sakin sa shi kuwa sai faman danna mata ashar yake yi. Lokaci kankani mutanan layin duk suka taru aka rasa wanda zai zo ya kwace ta domin kuwa suna tsoron TANGA ba wanda bai sanshi ba a fadin garin nan tattarin dan jagaliya ne kashe mutum a wajansa ba komai bane yayi zaman gidan kaso yafi a lissafa a fitowa dashi. "In kana yiwa Allah da Annabi ka bani hijabi na". Ta fadi cikin muryar kuka jikinta sai rawa yake yi wani takaici take ji a zuciya ji take kamar ta hadiye zuciyar ta mace. Cilli yayi da hijabin da sauri ta rarrafa za ta dauka ya danne mata yatsun hannu ta kurma uban ihu a daidai lokacin motar Dr.Karami ta sanyo kai ganin abin dake faruwa a layin ya sanya shi taka burki ya fito da sauri yana duban mutanan da sukayi cirko-cirko suna kallon rigimar Hafsat da Tanga da sauri ya isa wajan sam bai san wacece ba amma ganin irin cin zarafin da ake yi mata ya sanya shi zuwa ya hankaɗe tanga a daidai lokacin ita kuma Hafsat ta dago kai. 'Innalillahi' abin da Dr.Karami ya furta kenan yana ja da baya duban ta yayi kafin cikin hanzari ya isa ya dauko mata hijabin nata ya yafa mata a jikinta cikin sauri duban mamaki yake mata da al'ajabai ganin yarda ta koma kamar ba ita ba. "Hafsat me ya hadaki da wannan mutumin har yayi miki wannan cin zarafin?". Girgiza kai kawai take yi zuciyarta na suya hawaye sai ambaliya suke yi mata a fuska numfashi taja mai cike da takaici ta mike kan kafafuwanta ta dubi Tanga sannan ta dubi Dr.Karami a hankali ta raɓashi zata wuce gabanta ya sha yana mai sake tambayarta amma ta kasa bashi ansa kuka kawai take yi abin duniya ya yi mata yawa abin da bata so a gane yau gashi a bainar jama'a kowa ya gani kuma ya san halin da take ciki dama an dade ana zarginta yau dai gashi zargin ya tabbata kowa zai tsine mata da kazamar rayuwar da ta zaɓawa kanta wanda take ciwa mutunci take yi wa kallon banza ta sani yau sai sun zuba ruwa aka sun sha. Ihun da taji ne ya katse mata dogon tunanin da take yi cikin razana ta juya Dr.Karami ta hanga ya cakumi Tanga sai jibgarsa yake yi gabadaya ya kumbura masa fuska bakinsa har ya fashe yana zubda jini ware idanu tayi mamaki ya sake cikata da sauri ta ja jiki ganin hankalin mutane ya bar kanta ya koma wajan su Dr.Karami. Tafiya take yi cikin sauri-sauri kamar zata kifa hijabin sai harɗe ta yake yi tattareshi tayi sosai ta rike a hannu ta shiga jefa kafarta a duk in da taji ta dira idanuwanta sun kara kaɗawa sun yi jajir tana kokarin karya kwanar da zata shigar da ita gida suka yi arba da Abulle kallo ta bita dashi daga sama har kasa kafun ta dauke kanta cike da takaici da bakin cikin wannan rayuwar da 'yarta ta tsinci kanta a ciki Allah na gani tayi bakin ciki tayi takaici tayi kuka sosai a kan wannan lamarin zuciyarta ji take yi kamar za ta soye don raɗaɗin da take ji tun da abin nan ya faru ta kasa kwanciyar hankali kullum cikin fargaba take akan abin da zai je ya dawo. "Daga ina kike?". Ta fadi fuskarta a daure tamau kamar bata taba yin dariya ba ba alamun tausayi amma in da zaka fasa zuciyarta tausayin 'yar ta ta ne makil a cikinta. Girgiza kai Hafsat tayi hawaye na sake balle mata sautin kukan da take boyewa ya bayyana sosai hakan ya kara tayar da hankalin Abulle da sauri ta riko mata hannu tana mai tambayar ta cikin yanayi na firgici amma ta kasa magana sai girgiza mata kai take yi tana kai hannayenta saman bakinta tana toshewa. Riko ta tayi sosai ta sanyata gaba suka nufi gida tafiya suke yi gabadayan su zuciyoyinsu na suya musamman Hafsat in ta tuna cin zarafin da akayi mata a bainar jama'a sai ta sake rushewa da kuka kamar numfashinta zai dauke a soro suka ya da zango Abulle sai mai da numfashi take yi ita kuwa Hafsat zubewa kan gwuiwowinta tayi ta rufe fuskarta da tafukan hannayenta tana hadiyar zuciya sai shassheka take yi idanuwan nan nata sunyi luhu-luhu jikinta na faman kyarma. "Ya isa haka Hafsat dai na kukan fada min abin dake faruwa?". Dago jajayen idanuwanta tayi ta sauke su kan Abulle cikin wani irin yanayi muryarta na rawa ta shiga bata labarin abin da ya faru da ita a yanzu... Wani kuka ne ya sake kufce mata ta rarrafo ta riko mata kafa. "Don Allah Umma ki yafe mani na tuba wallahi ba zan sake ba ina cikin bala'in rayuwa ita cikin kazamar rayuwa wacce ni ne na zama silar faɗawa cikin ta don Allah ku yafe mani abin da nayi muku na san ban kyauta muku ba a matsayin ku na iyaye na...". Da sauri Abulle ta toshe mata baki tana mai duba kofar gidan da soron gidan ganin ba kowa ya sanyata duban Hafsat wacce gabadaya ta fice daga hayyacinta. "Hafsat kukan ya isa haka nan kiyi shiru karki haifarwa kanki da wata matsalar ciki ne a jikinki wannan kukan kuma da kike yi kina ta da hankalin ki sai ki fuskanci matsala...". "Nafi kaunar in shiga matsalar da zan mutu akan wannan rayuwar da nake yi na tsani wannan rayuwa na tsani wannan duniyar na tsani kaina...". Da sauri ta rufe mata baki ita kanta 'yarta ta tausayi take bata kwalla ne suk cika mata idanu da sauri ta kau da kai ta dauke su ta janyo Hafsat jikinta. "Ya isa haka ki daina fadin haka komai da kika ga yana samun bawa a duniyar nan ƙaddararsa ce haka...". "A,a Umma wallahi ba ruwan kaddara ni ne sila komai da yake faruwa dani ni ce sila kiyi hakuri Umma ku yafe mani na gaji da rayuwar nan nafi kaunar mutuwa da wannan rayuwar na san ko a wajan Allah ni mai laifi ce nayi abun da yake fushi dani nayi abin da ya kauce hanyar addini na kaico! Umma nasan na aikata kuskure Umma duk abin da kika ga yana faruwa Goggo ce sila ita take sanya ni". Da sauri ta sake rufe bakinta tana mai girgiza mata kai. "Nace kiyi shiru ko bana son jin komai daga gareki...". "Umma ki bari na fadi domin ni dai na san rayuwata ta kare gwanda na fadi komai domin ki rokar min afuwa wajan mahaifina da wanda ya zama ina da hannu cikin faɗawarsu hukubar rayuwa". Nisawa tayi tana mai da numfashi kafin ta gyara zaman da tayi dirshan akasa ɗan cikinta take ji yana ta faman juyawa yana tokare mata kirji laɓɓanta ta ciza gami da runtse idanu hakan da Abulle ta gani ya sanyata ware idanu tana tambayarta ko lafiya amma ta kasa bata ansa sai da ta dauki lokaci a haka kafun ta nisa wasu zafafan hawaye suka zubo mata. "Duk halin da su Mariya suka shiga da Ummanta Goggo ce sila haka bacewar Abban su Mariya Goggo ce sila ita taja ni muka je wajan wani mutumi a dajin kauyen Sulalla akayi masa kurciya...". "Innalillahi wa inna ilair raji'un". Abin da Abulle ke maimaitawa kenan tana dafe kanta da take jin yana kokarin rabewa biyu lokaci guda idanuwanta suka kaɗa sukayi jajir wata irin tsanar kanta take ji tana tsanar zaman ta a duniyar nan a daidai wannan lokacin wani takaici ne da bakin ciki ya turnuke ta bata san tsanar da Goggo tayi ma su Bello har ta kai haka ba ta san kiyayyar da take masu takai haka ba. Mikewa tayi kan kafafuwanta tana duban Hafsat kafin ta fidda hannu cikin zafin nama ta dauketa da Mariya hagu da dama har sai da ta tuntsira ta bugu da bango hancinta da bakinta duk sun fashe suka dinga zubda jini da sauri ta ja jiki zuciyarta na suya ta fice daga cikin soron zuciyarta take ji tana kara ya mutsewa gabadaya taji ta tsani zaman ta a duniyar ina ma numfashinta zai dauke ta rabu da wannan takaicin da bakinciki da uwarta da 'yarta suka cusa mata a zuciya. Hafsat ganin yarda Abulle tayi mata ta sake rushewa da kuka tana hada kanta da bango kamar ba a jikinta yake ba sai da tayi kuka ma ishinta sannan ta mike tana faman hade hanya ta nufi cikin gidan. ******** Fizgo shi yayi suka isa kofar gidan sai faman cin magani yake yi Alhaji Abdurrazaq ya kwala sallama hannunsa rike da Huzaif da gabadaya ya gama kumbura ji yake yi kamar ya fashe don takaici da bakin ciki wai mahaifinsa ya yi masa irin wannan cin zarafin akan wata banza wacce bai ganin ta da wata kima ko daraja. Abban su Mariya ne ya fito yana duban su daya bayan daya don bai san su ba Alhaji Abdurrazaq ne yayi masa sallama ya ansa shi cikin yanayi na son karin bayani. "Kai ne mahaifin Hafsat?". Bello ya gyaɗa kai yana duban Huzaif ganin yarda aka riƙe shi kamar wanda yayi sata shi abin har dariya ya so ya bashi. "Sunana Alhaji Abdurrazaq ni ne mahaifin Huzaif wanda ya ci zafin 'yarku ya keta mata haddi". Zaro idanu yayi sosai yana duban su zuciyarsa yake ji tana bugawa da sauri-sauri wani takaici ya kume shi da sauri ya juya cikin gidan dakin Goggo Marka ya nufa ba ko sallama ya shiga tadda ita zaune yayi ta hada tagumi can gefe kuma Hafsat ce ta dukunkune sai faman numfashi take ja tana saukewa. "Kunyi baki ku taho suna jiranku".. Yana fadin haka ya fita daga cikin dakin zuciyarsa na raɗaɗi gami da zafi ya jima yana takaicin wannan lamarin tun lokacin da ya gane wa idanuwansa ya tambaya amma Goggo Marka ta so ci masa mutunci tun daga wannan lokacin bai sake magana ba sai dai yaje har gidan Abulle ya hadu da mahaifin Hafsat suka zauna sukayi magana a nan ya san komai yayi bakin ciki sosai yayi takaici. Tabarma ya dauka yanufi soro da ita ya shimfiɗa sannan yayi musu iso har lokacin Huzaif na hannun mahaifinsa ya ki sakin sa zama sukayi amma shi Huzaif ya tsaya kerere a tsaye a daidai lokacin suka iso su kuma Hafsat tun da ta hango huzaif ta ji gabanta ya yanke ya fadi wani kallo ta ga ya watsa mata ita ma kallon ta watsa masa daga nan ta kau da kai. Alhaji Abdurrazaq ne ya muskuta ya dubi Goggo Marka da tayi wiri-wiri da idanu sai hada gumi take yi abi duniya duk yabi ya addabeta. "Maganar da mukayi kwana ki dake na cewa zan aurawa ɗana jikarki domin kuwa cin zarafin da yayi mata ba zan yarda dashi ba domin ba zan yarda ko 'yata ayi wa haka ba don haka shine nake so ku bashi aurenta domin ba wanda zai aureta bayan shi in kuma ba ku yarda ba ni zan shigar da wannan maganar kotu kuma zan tsayawa Hafsat kai da fata har in ga an kwatar mata hakkinta". Bello ne ya dube shi sosai yanayin sa ya burgesa yarda ya nuna ba yarda ba akan cin zarafin da ɗansa yayi wa Hafsat ba ya ji dadin haka sosai ko ba komai ya nuna shi mutum ne mai mutunci da sanin ya kamata duban Goggo Marka yayi kafun ya kau da kai. "Ba sai maganar taje kotu ba ni ina bayanka nima a matsayin uba nake ga Hafsat in dai ta haihu ni na aminci ya aureta sai dai kuma magana daya akwai sharaɗi na lura kamar dole kayi wa ɗan naka don haka zan masa gargaɗi in har ya aureta ya ci zarafinta ko ya kuntata mata wallahi tallahi ni da kaina zan shigar da maganar nan kotu sannan a sake tada tsohon duk wani cin zarafi da yayi mata". Wani kuka ne ya zo wa Hafsat mikewa tayi ta dubi Huzaif da yayi tsiru-tsiru da idanu sosai take jin har yanzu tana son sa bata jin zata iya rabuwa dashi duk da abin da yayi mata son sa ya zama jinin jikinta wanda hakan har yanzu ya kasa sanyata ganin laifinsa duban su tayi dukkan su kafin ta ja kafafuwanta da sukayi mata nauyi ta shige cikin gida.... *Kamala Minna*💞💞😘😘 [10/26, 9:20 AM] DEENY MINNA🙋‍♂:  UKU BALA'I NA. KAMALA MINNA. *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA SITTIN DA BAKWAI. Gumi ne kawai ke ta faman keto mata kamar wacce aka juyewa diron ruwa sai faman yamutse fuska take yi tana cizon laɓɓa gabadaya ta gama galabaita ta fice daga hayyacinta lokaci-lokaci take ajiyar zuciya ita kadai tasan bala'i da masifan da take ciki yau kusan kwana uku kenan tana jin ciwon a tsaitsaye amma na yau ya shafe na kwanakin da tayi. Jikinta har karkarwa yake yi buɗe idanuwanta tayi da suke runtse sun kaɗa sunyi jajir jijiyoyin goshinta sun fito sosai kamar shirya su akayi kan fatar goshinta hawaye ne suka kwaranyo mata karo na ba a dadi duban dakin tayi gani take yi yana juya mata sama na dawo kasa kasa na dawo sama sake runtse idanun tayi gami da yin wani yinkuri da ya sanyata sakin wata kara mai razanarwa kafun lokaci guda tayi luf! kamar ba ita bace tayi ihun ba. Goggo Marka ce ta fado dakin cikin hanzari tana dubanta ganin yanayin da take ciki ya sanyata saurin isa gareta rikota tayi tana faman duddubata kafun lokaci guda ta gano abin da ke wakana da sauri ta gyara mata zaman dirshan da tayi tana mai rike mata kafadu da sauri ta fizge kanta daga hannun Goggo Marka tana faman sakin wani wahalallan numfashi hawaye sai ambaliya suke mata a fuska. Sake kai hannu tayi zata rikota a daidai lokacin cikin nata ya sake juyawa wata irin zabura tayi gami da wancakalar da ita gefe guda kan ta ya hadu da gadon karfen dake gefen su da sauri ta ja da baya tana riko goshinta don sosai ta bugu lokaci guda wajan ya kumbure sosai duban Hafsat ta shiga yi idanuwanta suna kawo kwalla gabadaya ta gama rikicewa kanta gabadaya ya gama shiga duhu tunda Hafsat ta fara nakudar nan a tsaitsaye hankalinta ya kai kololuwa ba ta san lamarin zai kai ga haka ba wai yau Hafsat ce za ta haife musu abin kunya ɗan shege na gaba da fatiha ba ta taba dana sanin wannan lamarin da kaico ba kamar yau zuciyarta gabadaya ta gama karyewa da tashin hankali bata san yarda za tayi ba bata san wa za ta kai wa kukan ta a daidai wannan lokacin ba kowa ya juya musu baya musamman Abulle da gabadaya ta dauke musu kafa ta daina bi ma ta kansu ga gidan yanzu ita kanta kunyarsu take yi ta rasa dalili ko da yake ita kadai ta san abin da ta aikata a garesu sosai take jin zuciyarta na kara karye da komai na duniyar ma. Ihun da Hafsat ta kuma yi ne ya sanyata dawowa hayyacinta dubanta ta shiga yi a tsaye take sai faman ya kice kayan jikinta take yi tana jifa dasu laɓɓanta cikin baki sai faman cijesu take yi kamar ba a jikinta ba idanuwanta a rufe da sauri Goggo Marka ta ja gefe ganin al'amarin ya girmama waje tayi da hanzari tana faman hada hanya Umma ce ta fito ta dubeta ganin yanayin da take ciki ya tabbatar mata ba lafiya isa tayi gareta tana riko hannayenta ba abin da jikinta ke yi sai karkarwa. "Habeeba Ban san abin da ke faruwa da Hafsat ba ga ta can cikin dakin sai fizge-fizge take yi". Zaro idanu tayi tana ambaton innalillahi wa inna ilaihir raji'un da sauri ta saki Goggo ta nufi daki durkushe ta same ta sai faman nishi take yi ga wani mahaukacin gumi da ta hada gabadaya tayi jagaf! duban kasan ta tayi ganin ruwa na kwarara ya tabbatar mata haihuwa ce da sauri ta fice ba tare da ta taba ta ba can ta hango Goggo sai safa da marwa take yi hannu aka hakan yayi matukar bata mamaki yau kuma girgiza kai tayi gami da komawa daki mayafinta ta dauko ta yi hanyar waje. Tana sanya kai kofar gida ta hango su da sauri ta yo baya tana mai da numfashi ita gabadaya ta manta ma Mariya na waje lekawa tayi a daidai lokacin ita kuma Mariya idanuwanta na kallon kofar gidan don ta ga lokacin da Umma ta fito ta koma da sauri ya fito ta tayi da hannu sannan ta koma cikin soron sai faman kai kawo take yi don yanayin da ta ga Hafsat a ciki yayi matukar tsorata ta ba abin da ta tuna sai lokacin haihuwar Mu'azzam sosai zuciyarta ta karye lokaci guda hawaye su ka zubo mata a daidai lokacin Mariya ta iso ganin Umma da hawaye a fuska ya tsoratar da ita da sauri ta iso gareta tana tambayarta lafiya numfashi ta ja kafun ta runtse idanu jin yarda zuciyarta ke mikata wani yanayi. "Mariya Hafsat na cikin wani yanayi matuka haihuwar ce na ke zaton lokaci yayi amma yanayin da take ciki yana bani tsoro". Gaban Mariya ya yanke ya fadi idanuwa a waje. "Haihuwa!?". Ta fadi tana dafe kirjinta Umma ta gyaɗa mata kai da sauri ta juya tayi kofar gida wajan Dr.Karami ta koma kallo daya yayi mata ya gano tashin hankalin da take ciki da sauri ya iso daf! da ita kamar zai koma jikinta bakinsa har rawa yake yi wajan tambayarta lafiya runtse idanu tayi kafun ta buɗe su da kwalla hakan ba karamin kara tayar masa da hankali yayi ba. "Hafsat ce take wani mataki na haihuwa amma lamarin sai a hankal...". Tun kafin ta rufe baki yace da ita. "Muje!". Da sauri ta juya yana biye da ita suna shiga cikin soro suka tadda Umma wata irin kunya ce ta lullubeta shima Dr.Karami sadda kai yayi kasa don ba su yi tsammanin tadda da juna ba da sauri Umma tayi cikin gida shikuwa sai kokarin buɗe baki yake yi don gaishe Mariya ce tayi masa jagora zuwa cikin gidan dakin Goggo suka nufa wacce take bakin kofa lokaci-lokaci take daga labule tana duban Hafsat sai hawaye su zubo mata shar-shar. Daga labulan yayi ya shiga da sauri ya isa gareta ya dago kanta da ke sunkuye yana kiran sunanta amma ina ta kasa ansawa da sauri ya kalli inda take durkushe shiru yayi na dan lokaci kafun ya mike ya leka waje Mariya ya yafito dake tsaye ita ma cikin yanayin fargaba da hanzari ta iso gareshe. "Ku kamo ta kawai mu wuce asibiti ina ganin hakan zai fi dace wa don kin ga dai yanzu ko nace zan yi wani abu ba komai na aiki a wajena da zan taimaka mata domin ba a san yarda haihuwa zata kaya ba duk da dai gaf! take da yinta...". Wani ihu ne ya cika musu kunnuwa da sauri Dr.Karami da Mariya suka faɗa dakin a daidai lokacin kan jaririn ya sanyo kai ware idanu yayi kafun yayi waje da sauri cikin sakanni ya dawo hannayensa da safa a ciki duban Mariya yayi wacce ta runtse idanu har da rufe fuska da mayafin jikinta girgiza kai yayi kafun ya isa wajan Hafsat wacce sai faman nishi take yi na wahala da taimakon Dr.Karami cikin ikon Allah Hafsat ta haihu bayan ta gama kururuwa jaririn na fadowa ta ta baje a kasa numfashinta na fita kadan-kadan. "Mariya anso mani reza wajan Umma". Da sauri tayi waje ta isa inda Umma ke tsaye sai faman Addu'a take yi idanuwanta sun kaɗa Mariya na isa ta dubeta jiki a sanyaye. "Umma reza ake bukata". Da sauri ta faɗa daki ta binciko sabuwar reza ko buɗeta ba ayi ba ta mikata mata zuciyarta na rage fargaba tunda ta ga an anshi reza da alamun an haihu da sauri Mariya ta juya ta koma dakin tana mika masa ya buɗeta ya yanke cibi a daidai lokacin kuma mahaifa ta fado dauke jaririn yayi wanda ya kasance namiji kyankyawa dashi dube-dube ya shiga yi. Mariya ta lura dashi kuma ta gane abinda yake nima don haka da sauri ta kara so ciki dakin can gefe ta nufa inda wata akwaku take budewa tayi ta zaro wani sabon zani da alamun ko daura shi ba a taba yi ba ta mika masa goge jaririn ya shiga yi dashi sai da yayi masa tsaf! Sannan ta sake dauko wani ta mika masa ya nannaɗe shi a ciki ya mika mata komawa yayi wajan Hafsat ya dubata ganin yanayin da take ciki ya sanya shi yin waje da sauri Goggo Marka ya duba da ta gama firgicewa can gefe Umma ce ganinsa ya sanya ta yin kasa da kai. "Alhamdulillah ta sauka". Yana fadin haka yayi waje da sauri su kuwa har rige-rige sukeyi wajan fadawa dakin duban juna suka shiga yi kafun Umma ta shiga tsaftace dakin ta gyarawa Hafsat jikinta sosai ta tsorata ganin yarda ta karu a kasan ta hakan ya fadar mata da gaba duban Mariya tayi wacce itama idanuwanta na kanta gyaɗa mata kai tayi ba tare da tace komai ba a daidai lokaci Dr.Karami ya yi sallama suka ansa shi shigowa yayi hannunsa dauke da dan karamin kwanati (First Aid Box) cikin taimakon Allah yayi mata dinkin inda ta karu gami da allurai duban Umma yayi bayan ya ajje kunyar gefe. "Jininta ya hau sosai kar ku saka mata ruwan zafi yanzu a dai samu mai dumi ta wanke jikinta dashi sannan ga wannan magangunan...". Ya mikawa Mariya ledar yana mai cigaba da fadin. "In ta ci abinci sai ku bata ta sha tsarin na nan a ciki Mariya sai ki duba ki gani Allah ya raya ya ɗayyaba". Yana gama fadin haka ya mike yana duban Hafsat wacce ta dawo hayyacinta idanuwanta sai zubda hawaye suke yi ta kasa kallon kowa ma a cikin dakin yana kokarin fita yaji muryar Umma nayi masa godiya gami da Addu'a murmushi yayi gami da cewa 'Ameen' azuciyarsa sosai yaji dadin addu'ar a ransa. ***** A wulakance ya anshi jaririn da ta mika masa sai faman cin magani yake yi yana hararar Hafsat da kanta ke kasa ita kadai ta san yanayin da take ciki tunda ta haihu yau kwana uku kenan gabadaya taji komai ya canza mata bata jin dadin komai rayuwar ta take ji gabadaya ta gaji da ita zuciyarsa sai zafi take yi ruhinta kamar zai kama da wuta. "Meye haka Huzaif ya naga kana riƙe shi a wulakance ne kamar ba jininka ba ban son rashin hankali fa". Mahaifiyarsa dake zaune ta fadi dama tunda da ta mika masa jaririn ta ga rikon da yayi masa ranta ya ɓaci sosai ji take yi kamar ta mike ta kwada masa mari don sosai take jin haushin sa tun a gida don da kyar da dole sannan ya zo wajan ganin jaririn da Hafsat ta haifa masa. Sake turbuɗe fuska yayi yana dubanshi ya wullawa Hafsat wani mugun kallo cikin tsana da takaici abin da ke kara bata masa rai yarda jaririn yayi kama da shi sak! kamar kak'i yayi ya ajje hakan na kara kona masa zuciya domin kuwa bashi da wata mafita ko yace ba shi yayi ba ina ma zai ce bashi yayi ba ba yarda za ayi ba yarda ya ga kowa na gidan su ya dau zafi dashi akan Hafsat har sun fi kaunar ta dashi a yanzu. "Ka tafi ka kaiwa mahaifin naka shi ya ga jikansa". Ta sake fadi cikin ba da Umarni gabanshi yaji ya yanke ya fadi tunawa yayi da mutannan da suke soro a zaune ga Abban su Mariya ga nasa ga kuma mahaifin Hafsat wani irin ihu yaji kwanyarsa tayi saura kadan jaririn ya suɓuce a hannunsa da sauri ta kai hannunta ta na cilla masa mugun kallo. "Wai mai yasa Huzaif kake son bata min rai ne kai yanzus aboda rashin imani ɗan naka zaka yasar saboda wata banzar akiɗa taka da bata da madafa ko mafaka kasan Allah zan bata maka rai in baka yi wasa ba kuma ka rike shi ka mika musu shi tun kafin na bata maka rai". Da sauri ya juya ya fita ta bishi da mugun kallo kafun ta juya da idanuwanta ta dubi Hafsat dake ta faman zubda hawaye. "Kin ga irinta ko Hafsat duk macen da bata kama kanta ba har namiji yayi galaba akanta tana cikin masifa duk son da namiji zai nuna miki duk kaunar da namiji zai ce zai miki karki sake ki saki jiki dashi har wani abu ya shiga tsakanin ku domin duk namijin da ya kasance da mace ba tare da aure ba har ta yarda to wallahi ya daina ganinta da daraja da kima kenan yanzu dai kin ganewa idanunki wani uba ne zai dinga wulakatar da ɗansa har haka in da kunyi hakuri kunyi aure ba ku keta hakkin Allah ba duk haka ba zata faru gareku ba kuna da son zuciyarku so na rufe muku ido har kuyi sake Shaidan yayi tasiri akan ku kina dai kallon yarda Huzaif yake yi miki a yanzu wanda ni sam bana jindadin haka don ba zan goyi bayan sa ba ina so ki kwantar da hankali ki ajje komai a gefe ki fuskanci rayuwa ki raini ɗanki sannan ki dauki komai a matsayin ƙaddara a rayuwarki ta duniya kuma nayi miki alkawari in har auren nan naku ya tabbata ni zan tsaya miki ba zan taba yarda Huzaif ya cutar dake ba ko yaci zarafin ki". Dago idanuwanta tayi ta dubi Mahaifiyar Huzaif idanuwanta na kara rikicewa da zubda kwalla zuciyarta take ji tana kara yamutsewa wai ita ce yau namiji ke wulakanta wa bayan shine ya yi mata cin zarafin da ya zama bala'in rayuwa a gareta gaban kowa yake yi mata kallon tsana da k'yara ɗan cikinta da ya kasance jininsa shima bai tsira ba kaicon wannan rayuwa duban tsakar dakin tayi niki-nikin kayan da su kawo mata take bi da kallo kafun ta kau da kai ta cikin yanayi na zafin rai da kaicon wannan yanayi da ta tsinci kanta a ciki. Huzaif sai da ya gama safa da marwa a tsakar gida domin kuwa kunya ce gabadaya ta gama baibaye shi ya kasa zuwa ya kai musu jaririn duk abin da yake yi Mariya na laɓe a labulan dakin su tana kallon shi ji take yi kamar ta fita ta rufe shi da duka don takaici yarda taga yana duban jaririn yana harararsa ya bata haushi da sauri ta dage labulan ta fito wani firgita yayi don ya dauka mahaifiyarsa ce ta fito har zai kwasa da gudu jin gyarar muryar da Mariya tayi ya sanya shi tsayawa yana dubanta kallon sa ta shiga yi zuciyarta na zafi da raɗaɗi kafun ta dauke kanta ta koma cikin dakin fakare yayi da idanu yana kallonta kamar ya ga sabuwar halitta zuciyarsa yaji ta buga da wani irin yanayi kwanyarsa na ansawa runtse idanu yayi sannan ya buɗe a hankali ya taka kafafuwansa ya shiga cikin soron gabansa na yankewa yana faduwa yana shiga gabadaya suka zubo masa idanu ji yayi kamar ya nutse cikin kasa don kunya kafafuwansa sai harɗewa suke yi ji yake yi in ya kara taku daya zai baje a kasa mahaifinsa ne ya dubeshu da mugun kallo kafun ya ce dashi cikin daga murya mai cike bacin rai. "meye haka zaka zo ka tsayawa mutane a kai in ba zaka iso ba ka fita mana". Da hanzari ya iso gareshi gami da mika masa jaririn ansa yayi ya shiga dubansa kafun ya dago kai ya dubi Huzaif sak! kamar su ta bayyana a ransa ya dinga ina ma ina ma ace da aure ka samar masa wannan jikan da sai yafi kowa farinciki da jindadi a rayuwarsa amma ƙaddara ta rigayi fata. "Ƙayi masa huɗuba ne?". Ya fadi yana kallon Huzaif da yayi kasa da kai abin duniya duk yabi ya dame shi dago idanuwansa yayi ya sauke a na mahaifinsa yana girgiza kai. "Wa kake so to yayi maka wa ka mai da dan aikin ki haka za ka haifi 'ya'yan baka yi musu huduba don baka san darajar su ba?". "Ayi hakuri Alhaji miko min shi nayi masa ni zan wakilce shi". Abban Mariya ya fadi da murmushi a fuskarsa. "Da kan sa zai yi masa ko nan gaba ya koya". "Ba za ayi haka ba". Ya sake tarar sa, shi dai Mahaifin Hafsat abin duniya ne duk ya addabe shi ya kasa cewa kala sai bin su yake yi da kallo yana wurgawa Huzaif mugun kallo ji yake yi kamar ya mike ya rufe shi da bugu. "Wani suna za a saka masa?". "Tambayi shi rasa kunya din". "Hakuri za kayi". "Saka masa Muhammad Huzaifa". Dukkansu suka dube shi cike da mamaki Huzaif kuwa daskare wa yayi a kasa yanayin da suka ga Fuskar Alhaji Abdurrazaq ba wasa ba wanda ya tanka shi Abban Mariya yayi masa huduba sannan ya mika wa Mahaifin Hafsat amma sai ya kau da kai ya ki ansa ba yarda ya iya dashi ya mikawa Huzaif shi. "In tayi arba'in za a daura musu aure in Allah ya kaimu". Alhaji Abdurrazaq ya fadi ya harara Huzaif da ya mike jiki a sanyaye ya koma cikin gidan..... *Kamala Minna.*💞💞💞😘😘😘 [10/27, 11:01 AM] DEENY MINNA🙋‍♂:  UKU BALA'I NA. KAMALA MINNA. *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA SITTIN DA TAKWAS *BAYAN SATI UKU* Kai kawo kawai take yi tsakar dakin gabadaya ta gama firgicewa yau sati guda kenan ta rasa gane kanta tunda Dr.Karami ya sanar da ita zai turo iyayensa ta dauka abun wasa ne sai taga ya tabbata hakan ba karamin kara rikita mata lissafi yayi ba musamman da Abba ya turke ta akan tsakaninta da Dr.Karami duk da ya san komai amma sai ya matse ta sosai domin ta tabbatar masa da cewa Dr.karamin ne zabin ta ita dai Umma yar kallo ce har sukayi kidin su sukayi rawar su fata alheri kawai take yi don ta fi kowa farinciki da jindadin wannan lamari. "Wai ke lafiyarki kalau kuwa cikin kwanakin nan gabadaya na rasa gane kan ki?". Umma ta fadi tana duban Mariya numfashi ta ja kafun ta daga laɓɓanta tana koƙarin yin magana wayar Umma dake yashe ta dau kara tsuke bakinta tayi tana duban wayar ganin su Baseera ya sanyata saurin daukar wayar jiki a sanyaye. "Mariya kina ina ne?". Muryar Baseera ta karaɗe mata kunne ba tare da tayi sallama ba yanayin muryarta da ta yi maganar da alamun tsoro da fargaba numfashi Mariya ta ja kafun ta nisa. "Ina gida ya akayi ne?". "Wai kin ji yau za a kawo lefe inji Dr.Aqeel jiya yake sanar dani da daddare kin san shekarar jiya iyayensa sun zo tambaya". 'Innalillahi wa inna ilahir raji'un'. Mariya ta fadi a zuciyarta tana mai runtse idanuwanta kanta taji yayi mata wani gingirin gim! kamar an daura mata dutsen dala da goron dutse zuciyarta taji ta matse da wani irin yanayi komai take jin sa yana sauya mata ji take yi kamar ba ita ba komai take ji tamkar a mafarki yake faru. "Meye kuma haka ya za ayi kiyi shiru kuma kina jin ana zuke mata kudaɗen wayar ta ta". Umma ta fadi ganin yarda Mariya tayi mutuwar tsaye wayar a hannunta amma ta kasa furta komai kwanyarta take ji tana hautsewa da tashin hankali lamarin ne take ganinsa kamar ba gaske ba kalmar 'lefe' ce kawai ke mata hayaniya aka. "Nima haka take Baseera yanzu haka shirye shiryen da nake gidanku zan taho don bana son...". Shiru tayi tana duban Umma da ta kafe da idanu cike da zargi kau da kai tayi ta fara jan kafafu za ta fice daga cikin dakin Umma ita dai ido take watsa mata tun da aka fara maganar bikin nan na ta ta rasa gane kan 'yar ta ta komai nata ya sauya ga wani sanyin jiki da yake damunta ita dai ba ta ga abin damuwa a wannan lamarin ba abin farin ciki ya same ka amma gabadaya kuma sai ka sauya kamar mara lafiya. "...Uhmm fa kin san mi nima fa yau za su kawo anya Dr.Karami ba hada baki sukayi da Dr.Aqeel ace daga fara magana sai su zage suna kokarin rusa mana rashin mutunci nifa Allah na gani ban shirya ba...". Fizge wayar taji anyi da sauri ta juya Umma ce a tsaye fuskarta a hade kamar bakin hadarin dake kokarin zubda ruwa kasa tayi da kanta ganin irin kallo da Umma take yi mata nuna ta tayi da dan yatsan hannunta tana kokarin yin magana Bello ya shigo bin su yayi da kallo kafun ya dubi Mariya da kanta ke kasa. "Me kuma ke faruwa naga kun yi cirko-cirko da ku haka kamar zakaru?". Ba wacce tayi magana a cikin su Umma ta juya da sauri ta koma cikin dakinta duban Mariya yayi. "Ke me kika yi mata na ga ranta a ɓace?". Girgiza kanta tayi idanuwanta na kawo kwalla. "Ni ba kuka nace kiyi mani ba kin san natsani wannan hawayen naki ko don haka ki shafe su ki fada min abin da ke faruwa". "Ni ban yi mata komai ba Abba kawai dai...". Shiru tayi tana susar gefen kuncinta kafun ta dago kai ta dube shi shima ita yake duba kafun ya juya yayi cikin dakin Umma ya hango zaune ta zabga tagumi da sauri ya isa gareta zauna gefen ta gami da cire mata tagumi. "Me kuma ya hadaki da 'yar taki yau abin da ban taba gani ba?". Kallonsa tayi kafun ta dauke kai tana ajiyar numfashi. "Mariya har yanzu hankalin ta bai gama zama daidai akanta ba in ban da rashin hankali da wauta bayan an gama magana meye kuma na son mai da hannu agogo baya wai maganar nan fa ta kawo lefen take tayi wa kunci alamun bata son wai yayi wuri kaji fa shiririta". Murmushi yayi kafun ya shafi haɓarsa. "Da sauki in ba auren ne tace bata so ba duk labarin kanzon kurege take son biya miki ba wani abu ba". Ya fadi yana mikewa kan kafafuwansa dubansa tayi da mamaki. "Au haka ma zaka ce Abban Mu'azzam kasan dai halin yaran nan abin da kake ganin ba komai ba sai ka ga su sun girmama shi". Tsayawa yayi da tafiyar da yake yi ya juyo ya dube ta yana gyaɗa kai. "Bana so kina saka kokwanto a ranki don Allah ki daina in Allah ya yarda ba abin da zai faru sai alheri". Gyaɗa kai tayi gami da daga kafada tana mai da kallon kan Mu'azzam dake ta faman sheka barcin sa hankali kwance tashi tayi ta shiga kokarin gyara dakin domin ta san yau dai gidan sai abin da hali yayi ta san yanzu haka iyalan su Baffa da wasu tsirarun dangin Abban su Mariya na hanya domin su ne za su zo har da su za a anshi lefen. Fita tayi can ta hango Mariya tana cigaba da gyaran gidan ba ta yi mata magana ba ta bi sahunta lokaci kankani duk suka kammala komai nan suka hau girke-girken tarar baƙi. Sosai Mariya ta gaji domin ba su gama aikin ba sai wajan daya kuma karfe biyu yan kawo lefen za su zo so take yi ta bar gidan amma Umma ta kasa ta tsare ta hana ta sak! ji take yi kamar ta daura hannu aka ta kurma ihu musamman yarda ta ga Umma ta tsare mata gida ko magana kuma ba tayi mata tun da safen. Zaune take ta zabga tagumi sai faman tunanin yarda zata bar gidan take yi gidan su Baseera ta so zuwa to ita ma gashi an yi mata bazata an kwakuya mata rashin mutunci tana tunanin hadin bakin su ne Dr.Aqeel da mutumin nata. ******* Horn taji anayi mata sam! bata dauka da ita ake ba sai da taji abin yaki ci yaki cinyewa sannan ta tsaya gami da waigowa motar da ta gani ne hakan ya sanyata tsuke fuska tana kokarin cigaba da tafiyarta. Da sauri ya kashe motar ya fito da hanzari har da gudu gudu ya isa gareta gabanta ya sha yana kure ta da idanu ita mata kallonsa take yi kafun ta kau da kai tana jin yarda zuciyarta ke bugawa da sauri-sauri. "Ina zaki je bayan kin san dai yau rana ce ta musamman". harararsa tayi kafun ta dauke kanta hakan da ya gani ya so bashi dariya don ya san laifin sa yayi mata abun da ba ta san dashi ba shi kasan kasa rike kan sa yayi tun da aka yarje masa an bashi ita gabadaya ya ji kamar nan da wani lokaci wani zai kwace masa ita musamman in ya tuna irin TAQADDAMA da aka kwasa. "Ba laifi na bane laifin mutumin ƙawarki ne". Da sauri ta dube shi kafun ta motsa laɓɓanta kamar mai son yin magana amma ta fasa. Gyaɗa kai yayi fuskarsa da murmushi. "Har kun gama rigimar taku ne?". Ta tambaye shi idanuwanta cikin nashi dariya ya tuntsure da ita kafun ya sake dago kansa ya dube ta. "Rigima ai dama kece sanadi tun da kuwa kika yi masa tukuici ƙawarki komai ya koma normal tun ranar da abin ya faru ya sanar dani komai kuma mun yafi juna SHARRIN SO ne kawai dama ba wani abu ba". Da mamaki take dubansa kafun ta saki murmushi tana mai rufe fuskarta da hannayenta. "kin rufe fuska mana tunda kin hada zuciyoyi masu cike da ingantacciyar ABOTA suna rigima kamar mu abokai tun na makaranta amma ace a SANADIN 'YA MACE mun samu matsala abinda ya bani mamaki sannan na kara yarda SO ba abin da bai zai haifarwa zuciya ta aikata ba". ya fadi yana juya idanunsa da suke kara rikita mata lissafi. "Ina kika nufa naga kin fito a daidai wannan lokacin?". Juyawa tayi ta dubi Kofar gidan sannan ta dube shi tana yatsine fuska. "Ba zan iya zama bane su Baffa sun iso fa kuma hayaniya yayi yawa ni kuma bana so bayan haka kuma nasan yanzu...". Sai kuma tayi shiru ta kasa karasa abin da tayi niyyar fadi tana mai sunne kai kasa murmushi yayi don ya gano in da zancen nata ya dosa. "Zo muje ki raka ni tunda zaman gidan ne bakya so". Da sauri ta dube shi idanuwanta da wani irin yanayi kafun ta shiga girgiza kai alamun a,a shima mamaki ne ya cika shi ganin abin da take yi masa. "Saboda me ba zaki ba, ba fa nisa za muyi ba?". "Ka bar shi kawai ai ba dadewa za suyi ba nima makota zan shi akwai abin da zan yi ne". Ta fadi tana mai kokarin wuce shi ta tafi shan gabanta ya sake yi yana dubanta cikin idanunsa da suke kokarin sanya mata gajiya a jiki. "Baki yarda dani bane ko meye nufin ki?...ko da yake zo mu je to na kai ki gidan mutuniyar taki na san zaki fi sake wa a can din". Yana son takura mata ba ta son abin da zai dami zuciyarta so take yi ta tafi ta huta ko ta samu hutun kwakwalwarta don ta san tabbas in tabi Dr.karami surutunsa ya isa ya hanata sukuni ko kuma yayi ta yawo da ita ba su can shagon ba su can wajan shan Icea Cream ita kuma bata son yawa ce ya wacen nan. "Ina yini Dr.Karami". Kamar daga sama suka juyo muryar daga bayan su da sauri suka ji ya macece sanye da nikaf a fuskarta bayan ta da goye kallo daya Mariya tayi mata ta gane wacece kau da kai tayi a daidai lokacin ita kuma ta dage nikaf din Hafsat ce gabadaya ta rame tayi zuru-zuru da ita ga wani baki da ta kara yi kamar wacce ta jima tana jinya duban ta sosai yayi kafun ya gane ta murmushin yake ya saki yana ansawa. "A,a Hafsat daga ina haka da ranar nan". Murmushi tayi itama na yake duk ta sha jinin jikinta domin kuwa gabadaya kunyar Dr.Karami take a yanzu. "Wallahi Huzaif na kai asibiti ba shi da lafiya ". 'Huzaif' Ya fadi a ransa sunan nayi masa yawo kwanya kafun ya dawo tunaninsa ya sake yi mata magana har tayi gaba duban Mariya yayi wacce takure shi da mayun idanuwanta ta na jefa masa kallon mai dauke da yanayin bacin rai kau da kai yayi shima a zuciyarsa dariya yake yiwa Mariya ganin yanayin da ta nuna masa yaji dadin haka sosai ko ba komai ya hango kauna gami da kishinsa a tsakar idanuwanta. "Kallon na meye haka?". Ya fadi yana murmushi hakan ya kara tura mata haushi sake tsuke fuska tayi tana kokarin wuce shi da sauri ya kai hannu zai riko mata hijab mai ya gani kuma yayi saurin janye hannunsa zuciyarsa na bugawa ba zai taba manta yarda suka kwashe da ita ba lokacin da ya rike ta bisa kuskure in kuwa ya sake maimaitawa a yau ya san zata dauka a gaske yayi Allah kadai ya san hukuncin da za tayi masa numfashi yaja daidai lokacin da yaji tsayuwar motoci ita kanta Mariya tsayawa tayi da tafiyar da take yi ta juyo ganin motocin sunyi parking kure su tayi da idanu gabanta taji ya yanke ya fadi ta tabbata yan gidan su Dr.Karami ne masu kawo lefe don haka da sauri ta juya ta dube shi ganin yana yi mata dariya har da gwalo ya sanyata turo baki gaba tana harararsa kafun ta juya da sauri ta fada gidan makotansu. Shi abin ma dariya ya bashi bai san wacce irin kunya bace Mariya gareta ko da yake jinin fulani in yayi duba da Umma sak! ita ma haka take da sauri ya shiga motarsa ya ja ya isa inda motocin suke mazaje ne ziryan ba Mace ko daya a cikin su sune yan kawo lefen. Gaida su yayi bayan ya fito daga cikin mota wani kanin Hajiyarsa ce ya kalle shi cikin harara. "Au wai ke dama kana nan unguwar ko biye damu kake?". So sa kai yayi kafun ya dubi sauran yan uwan mahaifin nasa da sukayi masa kuri da idanu suna dariya. "Kawu Sako fa na kawo mata shi...". "Sako eh tabbas na ga sako ai sai ka zo muje Lefen ma mu kai da kai tare ko". Gabadayan su suka kwashe da dariya a hankali ya ja da baya kansa akasa ya fada cikin motarsa ya yi mata Key sannan ya leko da kai waje. "Kawu sai kun dawo a dai yi duk abin da ya kamata surukar taka ta musamman ce". Ya fizgi motar da gudu yana faman sheka dariya suma dariyar suke yi kafun su bude kofofin wata mota kirar Benz sabuwar dalla sai daukar idanu take yi suka shiga sauke tika-tikan akwatina masu kyau da tsari har set biyu kallo daya za ka yi musu ka kasa dauke idanuwanka domin sun hadu iya haduwa tsayawa masalta su wani cin lokaci ne da nuna kauyanci... *Ina Yan Team din Dr.Karami da Mariya lokaci fa ya zo ku zo ku fara shirye shiryen biki ku fidda mana da Anko domin biki mai ansa sunansa biki za ayi* *Haka ma Yan Team din Dr.Aqeel da Baseera Ku shirya shagalin ku*😀😀 A gefe guda ga bikin su *Hafsat mai jego da angon karni Huzaif...lol*😀😀 *Kamala Minna.*💞💞😘😘😘 [10/28, 8:42 AM] DEENY MINNA🙋‍♂:  UKU BALA'I NA. KAMALA MINNA. *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA SITTIN DA TARA. Dubansa take yi zuciyarta na kara mikata wani mataki na son sa duk cin mutunci da wulakanci da yake yi mata sam bai damunta kamar yarda yake bayyana kiyayyarsa gareta sosai take jin zuciyarta na suya ruhinta da kwanyarta ja take kamar za su kama da wuta numfashi take ja a hankali idanuwanta sai zubda hawaye suke masu zafi ta duɓe shi a karo na ba a dadi hannunta rike da Huzaif. "Huzaif yau ni ce kake wulakanta wa Huzaif yau ni ce kake ciwa mutunci bayan kai ne silar faruwar komai gareni...". Wani banzan kallo yayi mata kafun ya mika mata Huzaif dake hannunsa dama duk ya gaji da rikonsa ji yake yi kamar an daura masa ƙaya a hannu in ba don Hajiyarsa tayi masa umarni da cewa ya dinga zuwa ba in ba haka ba zata bata masa ba abin da zai kawo shi wajan banzar yarinyar nan da bai san ma ya akayi ya fara kulata ba a yarda yake na matashi mai jini a jika amma ace shine yake tsayawa da wannan kazamar har za ta zama matar auren sa nan da sati guda. Wani kunci ne ya mamaye zuciyarsa ji yake yi kamar ya sheka ta ta mutu kowa ma ya huta. "Karki sake daura min laifi don bani na kawo ki ba ke kika kawo kan ki gareni sannan ban yi miki dole ba balle kiyi tunanin ko na KETA HADDI a gareki". Runtse idanu tayi tana jin yarda maganganunsa ke ratsa zuciyarta da kwanyarta suna haifar mata da wani yanayi mai kokarin kona mata duk wani sassa na jikinta girgiza kai ta shiga yi numfashinta sai kai kawo yake yi kamar zai dauke. "Ki rubuta ki ajje ko da kin aure ni wallahi ba zan taba son ki ba bana kaunar ki daidai da kwayar zarra a zuciyata domin ni ba zan auri jahila...". "Ya isa haka Huzaif ya isa nace maka!". Hafsat ta fadi cikin karaji tana toshe kunnuwanta da take jin maganganun kamar za su fasa mata su kuka ne ya sake kwace mata duban sa tayi. "Ba sai ka gaya min baka kauna ta ba sannan ba sai ka gaya min ka tsane ni ba amma ka ajje wani abu a ranka wallahi tallahi Huzaif sai na aure ka kuma wallahi sai ka so ni a yarda nake don ba wanda ya bata min rayuwa sai kai ba wanda ya jefani cikin bala'i sai kai don haka wallahi tun da muka dama tare da kai sai mun shanye sai dai in an kai ni gidanka ka dinga yagar nama kana watsarwa". Ta fadi tana hadiye kukan Huzaif ta saba abaya ta goyashi sannan ta sanya hannu ta shafe fuskarta da hawaye suka ki tsayawa da zuba wani abu ta hadiye mai tauri kafun ta dubi Huzaif da yayi fakare yana kallonta wani kunci da takaicinta na kara turawa zuciyarsa bakin ciki murmushi ne mai ciwo ya wanzu a fuskarta. "Kasan Allah Huzaif sai na aure ka a baya ina jin takaicin cin mutuncin da kayi mani bayan ka keta mani haddi amma tun da abin naka haka ne MU ZUBA MU GANI shege ka fasa". Da sauri ta juya zata tafi sai kuma ta tsaya zuciyarta na bijiro mata da wani tunanin juyowa tayi ta dube shi da mugun kallo a fuskarta goyon ta kwance sannan ta iso in da yake tsaye mamaki duk ya gama cika shi ganin yarda lokaci guda Hafsat ta juye kamar ba ita ba gaban motarsa ta isa ta ajje jaririn kafun ta dube shi hawaye na kara balle mata. "lokacin da muka hadu da kai ni kadai ka gani ba tare da wannan jaririn ba". Ta nuna Huzaif da yake ta faman wutsul-wutsul da kafa kafun lokaci guda ya balle da kuka. "ka dauke shi don bani ni ne ya kamata na rike shi ba a halin yanzu ka je kai ma ka ɗanɗana abin da ake ji". Tana gama fadin haka ta juya da sauri ta shige cikin gida kunnuwanta sai faman ansa sautin kukan ɗanta suke yi wani irin yanayi take jin kanta a ciki gabadaya duniyar take ji ta sure mata ina ma ace za ta mutu da sai tafi kowa farin ciki. Kwalla mata kira yake yi amma ina ko ta kan sa ba ta bi ba juyawa yayi ya dubi Huzaif ganin yarda yake rusar kuka gabadaya yaji ya firgice da sauri ya isa gareshi ya dauke shi yana jinjigashi amma ina kamar ana kara rura wutar kukan nashi waige-waige ya shiga yi amma ba kowa a layin da sauri ya isa kofar gidan ya tsaya idanuwansa sunyi tsuru-tsuru gabadaya kwanyarsa yake ta rikice kafun ya ankara yaji saukar fitsari a jikinsa wani ihu ya saki yana daga shi daga jikinsa fitsari sai tsartuwa yake yi hakan ya kara bata masa rai ya shiga yatsine fuska ji yake yi kamar yayi cilli da jaririn amma ya kasa ya leka soron yana zundumawa Hafsat kira amma ina kamar yana kiran dutse tana jin sa amma tayi banza dashi zuciyarta kuwa sai zafi take yi in ta jiyo kukan ɗan nata ji take yi kamar ta tashi ta anso shi amma in ta tuna abin da Huzaif yayi mata sai ta komata zauna tana rusar kuka. Mota ce kirar Benz tayi Parking a daidai kofar gidan su Mariya da Baseera suka fito daga can gefen direba kuma Dr.Karami ya fito fuskarsa da yalwataccen yanayin farin ciki duban su yake yi su duka kafun ya sauke akan Mariya da tayi kasa da kai Baseera kuwa sai zabga dariya take yi tana duban Dr.Karami da yake harararta. "Malama ba ma son ranin sense ga ya za ayi za ki dinga mana dariya". Ya karashe shima dariya na kokarin kwace masa a daidai lokacin Mariya ta dago kai ta dube shi tana watsa masa harara. "Malama zo mu wuce ciki in kun gama dariyar". Mariya ta fadi tana duban Baseera Dr.Karami ne ya miko musu jaka mai dauke da IV Baseera ta ansa tana dubawa kafun ta mikawa Mariya. "Naki yafi nawa kyau gaskiya". "Ai sai ki sauya". Ta fadi tana harararta sake tuntsirewa da dariya Baseera tayi kafun ta ja hannun Mariya su fara tafiya. "Au ko sallama babu da yake nayi muku abin da kuke so ko, ai ko ni direbarku ne sai haka inda na san haka Allah sai dai naki Dr. ya zo yayi wannan yawon dake amma saboda son kai ya tashi ya gudu ya barni da iyayinki". Dariya ta sake yi kafun ta dubi Mariya da gabadaya ta ki sakin jikinta sai faman hade fuska take yi. "Kai ka san in da ba abin da ya sanya shi gaba ba abin da ba zai mani ba kuma ko da ka tafi dani ai na taimaka maka ita mutuniyar taka mai tayi bayan zaman shiru komai ni nake yi". Tana gama fadin haka ta ja Mariya sukayi gaba bin su yayi da kallo zuciyarsa na mika shi wata duniya ta musamman sosai yake jin zuciyarsa na kara narkewa da wani irin yanayi game da Mariya ji yake yi kamar ya sake janyo lokacin bikin ya dawo nan da kwana biyu ba sati guda ba. Sai da ya ga shigewarsu sun sha kwana sannan ya shige motarsa cike da farin ciki ya ja ya tafi. Turus suka tsaya a kofar gidan ganin abin da ke faruwa Baseera ce ta dubi Mariya baki na rawa. "Mugun abu Mariya me nake shirin gani?". Wani yaƙe Mariya ta saki kafun ta dubi Huzaif da yayi wujiga-wujiga dashi gabadaya jikinsa ya gama bacewa da fitsari da kashin ɗan nasa fuskarsa kawai zaka kalla ya baka tausayi don gabadaya yayi laushi ji yake yi kamar ya kurma ihu don takaici sam bai lura da su Mariya ba sai da suka iso kofar gidan za su shiga ya gansu ji yayi kamar ya nutse a kasa don kunya duk sai yayi wani wiƙi-wiƙi dashi kamar wanda yayi wa sarki karya Baseera kuwa abin dariya ya bata amma sai ta kanne dama ta dade tana jin haushin Huzaif tun lokacin da ta samu labarin abin da ya faru tana kokarin yin magana taji Mariya ta fizgi hannunta sun faɗa soro da sauri ya bi bayan su yana kwalawa Mariya kira cikin wani irin yanayi na rawar murya tsayawa tayi cak! batare da ta juyo ta dube shi ba. "Don Allah taimaka ki mikawa Hafsat ɗan nan tun dazu yake ihu na kirata amma ta ki zuwa ban san mai take nufi ba". Baseera ce ta juyo ta dube shi a wulakance. "Meye nata ita da kake cewa ta anshe shi ta kai shi ai na dauka gidan ba bakon ka bane ko ai sai ka shiga ka kai shi ba ma wannan ba ai na dauka ɗan ka ne ka ga ai kaima zaka iya zama ka rarrashe shi ba dole sai uwarsa ba". Runtse idanu yayi domin sosai yaji maganganun Baseera sun taba masa zuciya amma sai yaki nuna haka a fili sai ma murmushi yaƙe da yake ta faman yi yana sanɗa kai domin ba abin da yafi bukata a yanzu illa a raba shi da yaron nan don ya gama firgitashi gabadaya musamman in ya dubi jikinsa yarda ya baci duk abin duniya ya bi ya dame shi. "Don Allah na roke ki". Ya fadi da muryar tausayi ganin Baseera ta ja hannunta za su shige juyowa tayi ta dube shi. "ka bari za a turo maka ita sai ta anshe shi da kanta ban san abin da ya hada ku ba har ta bar ɗan nata a nan ba zan asa taje taga baƙina ba". Tana fadin haka ta juya suka shige shi kuwa ji yayi kamar ya kurma ihu don takaici sai ya tafi kamar zai shiga cikin gidan sai kuma ya dawo da baya. Suna isa cikin gidan suka hangota can kofar daki ta hada kai da gwuiwa sai shsashekar kuka take yi Baseera ta dube ta ta taɓe baki kafun ta saki hannun Mariya ta fada dakin Umma. " Bai kamata ace kin zo nan kin zauna kin barshi rike da ɗanki ba ya kamata kisan darajar ɗa kuka yake yi fa amma kin zo nan kin zauna ai ko mai yayi miki shi Huzaif din bai kamata ki haɗa hukucin da zakiyi masa har da ɗan naki ba domin shi bai san komai ba bai ma san abin da kuke yi ba don haka ki je ki anso shi don ya ɓata masa jiki sosai". Tana gama fadin haka ta juya ta shigewarta dakin Umma zuciyarta na kara tausayawa yanayin da Hafsat take ciki gabadaya ta sauya kamar ba ita ba Mikewa tayi tana faman tankaɗi kamar wacce ta kwana ta wuni bata sakawa cikinta komai ba a hankali take tafiya har ta isa soron yanayin da ta ga Huzaif din a ciki sai da zuciyarta ta harba da sauri ta isa gareshi ta anshe shi tana wurga masa wani kallo kafun ta juya ta koma cikin gida ranta ba dadi gabadaya. Umma ce ta dube su su duka kafun ta dubi ledar da Baseera ta ajje gefe guda. "Wannan kuma na meye...ba ma wannan ba ina kuka tsaya tun dazu ku da kuka ce mani ba daɗewa za kuyi ba". Ta karashe tana duban Mariya da ta koma gefe ta takure kamar wacce bata da lafiya. "Wallahi abin da muka je ansowa ne muka samu ba a karasa ba". Baseera ta fadi tana zaro Iv din tana mikawa Umma ansa tayi tana dubawa kafun ta dubi Baseera. "Amma fa sunyi kyau sosai". Murmushi Baseera tayi kafun ta dubi Mariya wacce itama izuwa lokacin ta dago kai. "AMAREN BANA". Baseera ta fadi cikin zolaya hararar ta Mariya tayi kafun ta dubi Umma. "Ya kamata Umma ki yiwa Mariya magana gabadaya taki sakin jikinta shi kansa Dr. sai da ya tambaye ni ko akwai abin da ke damunta ne nace masa a,a gaskiya yanayin da take nunawa kamar akwai abin dake damunta". Numfashi Umma ta ajje kafun ta dubi Baseera. "Ni ban san ta ina zan fara miki ba nima yanayin da Mariya take nunawa ya fara isa ta wani in ya ga haka sai ya dauka kamar auren dole za ayi mata..." Bata karasa maganar ba wayar Baseera ta dau kara da sauri ta zarota daga jaka ganin sunan Mami ya sanyata saurin mikewa. "Umma bari na tafi kin ga har Mami ta kira ni nasan tana can tana jira na itama daɗewar da mukayi yayi yawa". Tana fadin haka ta dauki jakarta da ledar IV dinta ta fice bayan ta yiwa Umma Sallama Mariya ta mike jiki a sanyaye tayi mata rakiya.... *Kamala Minna*💞💞💞😘😘 [10/29, 9:38 AM] DEENY MINNA🙋‍♂:  UKU BALA'I NA KAMALA MINNA. *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA SABA'IN Runtse idanunta take yi zuciyarta na zafi ji take yi kamar ta haɗiyi zuciyarta ta mutu don bakin ciki kukan da take yi tana samun sauki a yanzu ya zama wahala a gareta HAWAYEN ZUCIYA da take jin zubar su suma tana samun sauki kadan suma sun dai na zuba idanuwanta gabadayan sun kekeshe ba alamun za su zubda hawaye zafin zuciya ne da na ruhi kawai take jin su kamar a wuta aka jefa ta. Dago kanta tayi ta dubi jikinta wani kunci ne ya sake mamaye zuciyarta in ta tuna yarda ta ga Mariya a wannan rana cikin yanayi na alfarma da shiga ta burgewa a matsayinta ta amaryar gobe har da ita amma ita ko wacce ta fi kowa rashin gata a duniyar nan sai ta fita jindadin irin wannan ranar wai ita ce yau kayan ma da zata saka ta fito a matsayinta na wacce za a daurawa aure amma sun gagareta kaicon wannan rana. Sautin guɗar da taji ta karaɗe gidan ne ta daki kunnuwanta ya sanyata sake runtse idanunta gami da toshe kunnuwanta ji sautin take kamar ana zirara mata ruwan dalma cikin kunnuwanta mikewa tayi kan kafafuwanta tana faman haɗe hanya fuskarta kadai zaka kalla ka gane kuncin da take ciki duban Huzaif tayi dake kwance a yan kwane kamar wanda ya fado daga sama ba uwa ba uba kau da kai tayi tana taka kafafuwanta tana kokarin fita a daidai lokacin Goggo Marka ta sanyo kanta cikin daki cikin yanayi na razana saura kadan su yi gware idanuwansu suka sarke da juna idanun Goggo Marka lokaci guda suka kawo hawaye da sauri ta kau da kai tana karasawa cikin dakin tayi zaman yan bori gami da dafe kanta wani irin kunci da takaici suke nukurkusar zuciyarta ga wani raɗaɗi da zafi da take jin ruhinta na yi mata kwanyarta take ji na ta faman ihu da hayaniyar abin da ya jefata cikin wannan halin bata taba zaton rayuwa zata juya mata haka ba bata taba zaton duniya zata yi mata gwatson mage ba sai yau. Dago jajayen idanuwanta tayi ta sauke a fuskar Hafsat wani irin tausayinta take ji na kara narkar mata da zuciyarta tana kaico da wannan rayuwa da suke ciki wacce ita ce ta zamo sanadi garesu baki daya ita ce silar faruwar duk wani bala'i da masifa da suka tsinci kan su. "Kiyi Hakuri Hafsat ki yafe mani NA YI NADAMA...". Wani banzan kallo ta wurgama mata dama cike take da ita tun jiya da ake ta shagalin baki tana kallonta ta kwashi jiki ta shiga tana farin ciki ita kuma ta barta da kayan takaici makale cikin daki sai dai in mutuwa za tayi tayi kenan haka a shekaran jiya Huzaif ya zo suka kai ruwa rana akan bikin nan nasu akan haka yayi fushi uban komai bai bata ba kuma duk Goggo Marka ce sanadi dan kayan ma da ake yi cewa yayi ba zai yi ba ita kuma bata so ta hadashi da iyayensa saboda yanayin da suka nuna mata ba ta so ta nuna masu yanayin da suke ciki da ɗansu domin ɗa da iyaye Allah ne kawai ya san tsakanin su tana tsoron su canza mata da ga kulawar da suke bata. "Me zaki fada min Goggo ai kin rigaya kin gama cuta ta ba abin da zan ce da ke sai Allah yayi mani sakayya ba wanda ya jefani cikin bala'in rayuwa sai ke ba wanda ya zaɓa min wannan kazamar rayuwar sai ke bani ga karatu gani da dan shege ga shi mijin aure ma wulakantani yake yi tun kafin naje gidan sa wannan UKU BALA'In da mai yayi kama ni dai na san na gama ASARAR RAYUWA a filin duniyar nan". Wani kuka ne ya kwace mata da sauri ta zame bayanta na kartar bango ta zube kan kafafuwanta wani kuka ne mai cin rai take yin sa amma idanuwanta kemadagas ba alamun hawaye runtse idanuwanta take yi tana buɗe su so take yi kawai ta buɗe su ta ganta a wata duniyar ba wannan ba... Sallamar da ake kwaɗawa tsakar gidan ya sanya su duban junansu jin ana ambatar Hafsat da sauri ta fice ta leka ganin tsirarun mutane yan biki suna ta kai kawo sai wasu mata biyu da suke tsaye wanda kallo daya zaka yi musu ka gane cikakkun masu ji da kan sune gaɓadayan su sai wani yatsine fuska suke yi suna taunar cingam gaban Hafsat ne ya yanke ya fadi kafun ta juyo ta dubi Goggo da tayi fakare da idanu. Da sauri ta fice daga cikin dakin gabanta na cigaba da buguwa ta isa garesu dubanta sukayi tun daga kasa har sama kafun su watsar dayan ta ja tsaki gami da tsartar da yawu hakan ya jawo hankalin yan bikin da suka fara taru har da na dakin Umma duk sun fito. "Kece Hafsat?". Babbar ciki ta tambayeta tana nunata da hannun hagu daga kai Hafsat tayi gabanta na kara tsinkewa ganin irin kallo da suke watsa mata a sa'ilin da ta tabbatar musu ita ce Hafsat din. "Da farko dai ni sunana Assama'u yayar Huzaif wanda kike fata ya zama mijin ki ta ko wani irin hali sannan ina so in sanar sake cewa ki shirya zaman kunci da takaici a gidan sa sannan ki sani mu zuri'armu ba 'yar iska sannan babu wacce tayi yawon ta zubar har ta samu kyautar tukuicin ɗan shege na gaba da fatiha wanda kika likawa kanina kika ce shine sanadin sa". Gabadaya mutanan gidan idanuwansu yayo waje don wasun su da yawa ba su san abin da ke faruwa ba abin ka da mata nan aka fara kuskus ana duban Hafsat wacce ta gama sankarewa a tsaye gabadaya ta ji duniyar na juya mata kafafuwanta take ji suna lauye suna kokarin zubda ita kasa numfashi taja mai tafe da zafin zuciya duban su ta shiga yi daya bayan daya kallon da suke mata mai cike da tsana da kiyayya ya kara tsinka mata zuciya. "Na san ba komai ba ne ya sanyaki makale masa har kika kunsa masa wannan sharrin saboda an ga gidan dala an ga gidan da jar miya ke kai kawo ba a saba lasa ba mai dattin hula ba ya kawo shine za a makalewa ɗan mutane to ki rubuta ki ajje bar ganin hajiya da Alhaji na goya miki baya to kisa ni ba da su za ki zauna ba da ɗan su za ki zauna har ɓarin jiki kike karen ki ya kamo zomo to wallahi zaki ya kawo miki wanda zai zaɓa miki UƘUBAR RAYUWA a gareki". Dayar ta fadi tana watsowa mata ledar dake hannunta gabadaya kayan suka zube a jikinta daidai nan wasu hawaye na takaici suka surnano mata a saman kunci gabadaya ta kasa motsi jin komai take kamar a mafarki ba gaske ba dafa kafaɗar ta taji anyi a hankali ta juyo Goggo Marka ce tsaye ita ma idanuwanta na zubda hawaye duban matan tayi cikin jin haushi kafun ta hadiye wani abu da ya tokare mata zuciya. "Rashin arzukin har ya kai haka ai ba karya akayi ba shi Huzaif din ai ya san shi ya lalata mata rayuwa don haka ya kamata ku gyara kalamanku sannan ku sani ba a 'yar iska daya dole sai an samu dan iska...". "Tsohuwar alagidigo tsohuwar banza gayyar kwadayayyu kisan dai ba yarda za ayi namiji ya tursasa mace akan wani ra'ayi ko dole sai ta aminta abu ke tabbata don haka karki sake karki sake dorawa Huzaif kalmar dan iska domin wannan karuwar 'yar taki ita ce silar komai". Gabadaya gidan ya dau salallami Umma dake tsaye bakin kofa idanuwanta sun kawo hawaye da sauri ta iso garesu ta shiga ba su hakuri da su tafi amma ina kamar kara ingiza su ake yi nan suƙa shiga hayaniya suna tsinewa Hafsat da Goggo Marka a cikin wannan yanayin Abulle tayi sallama ta shigo hankalinta yayi matuka wajan tashi ganin abin da ke faruwa da sauri ta isa ga Goggo Marka dake ta faman rusar kuka kamar ranta zai fi janye ta tayi ta kai ta daki kafun ta fito idanuwanta itama sun kaɗa sun yi jajir ta dubi Hafsat ta watsar domin kuncin da take ji a ranta akan Hafsat ji take yi kamar ta hauta da bugu domin komai ya faru duk ita ta jawo musu. Rigima ce ta balle sosai gidan biki ya hautsi ne sai da akayi da gaske bayan Umma ta kira Abban su Mariya ganin abin ya ki ci yaki cinyewa sannan komai ya lafa yan uwan su Huzaif suka fice Hafsat ta koma daki cike da takaicin wannan rayuwa da ta faɗa nan gidan biki lamari ya sauya nan da nan batun Hafsat ya zagaye ba abin da ake tattaunarwa akai sai maganar cikin shege da tayi Abulle ganin abin ya girmama kasa zama tayi ba tare da kowa ya sani ba ta fice daga cikin gidan cike da ɗacin rai. **** Sosai wajan ya tsaru tun da ga Get din in ka kalla zaka gane ba karamin waje bane aka kama domin shagalin bikin kamu na yau da za ayi tsaruwar ciki kuwa ba a magana ko ta ina haske kwayaye ne ke walwali kamar a kasar turai ga wani daddaɗar kamshi mai sanyaya zuciya kawai ke tashi ga wani CoolMusic dake ta faman tashi yana kara jefa al'ummar dake wajan kara faɗawa kogin nishadi sosai wajan ya ƙawatu da kayan alatu na more rayuwa ga wasu lafiyayyun kujeru za gaye da wani hadadden Table mai shimfiɗe da wani kayataccen yadi mai kalar Pink sai a tsakiyarsa an ajje wata fulawa mai kyalli da daukar idanu. A daidai lokacin da jama'a suka gama hallara ana jiran amare su ido Mc sai faman zubda zance take yi da yake mace ce KHADEEJA S MUHAMMAD yarda ka kusan taci bakin aku kawai nishaɗantar da mutane take yi ana ta dariya a wannan lokacin aka fara sanar da cewa amare sun iso a hankali Mc ta sanya Dj ya canza kiɗa wani lafiyayya sauti ya shiga tashi ga duka na faman ratsa jikin yan biki nan suka shiga gyaɗa kai suna rausayawa hankalin su gabadaya ya koma kan kofar Hall din wani turirin kamshi ya shiga fesowa kawayen amarya guda biyu daga gaba suƙa shigo hannayensu dauke da kaskon turaren wuta suka shiga zagaye wajan da shi kafun cikin sakanni AMAREN BANA Mariya da Baseera suka sanyo kai cikin Hall din da yake hada bikin akayi waje daya. Sanye suke cikin wani tsarren material Mariya ta saka Yellow colour ita kuma Baseera ta saka Light-Blue fuskokin su kawai zaka kalla ka gane suna cikin farin ciki da nishaɗi ratsantsiyar kwalliyar da akayi musu ta kara bayyanar da kyan su. Nan da nan waje ya hargitse shewa kawai ake yi sauti na cigaba da tashi a cikin wannam yanayi har suka iso mazaunin su suka zauna sannan Mc ta bada umarni a tsayar da kiɗa nan ta shiga jawabin da abin da ya tara su a wajan kafun ta nemi daya daga cikin yan biki ta zo ta buɗe taro da Addu'a Anty Yusra ce ta fito yayar Baseera tayi addu'o'i na neman yin taro lafiya a tashi lafiya sannan ta goɗewa duƙ wanda ya samu damar zuwa wannan bikin daga nan kuma lamari ya sauya a ka shiga biki gadan-gadan Malam Sanah S Matazu aka gayyata ta gwangwaje amare da wa'azi da duk wasu karin haske na zaman gidan miji da nuna masu hanyoyin na salo salo na kula da miji da yi masa biyayya sannan da hakuri da juriya da boye sirrin miji sannan da girmama iyayen miji da yan uwansa da duk wani majibancin sa wa'azi sosai tayi musu mai ratsa zuciya da jiki tsayi lokacin mai nisa kafun daga bisa lamari ya sauya sosai da sosai kamu ya ƙawatu sai son barka nan ka shiga ciye ciye da shaye shaye kafun wani lokaci kuma komai ya zama daidai misalin karfe shida da rabi a ka tashi na yamma domin mazajen sun ce ba su yarda su kai dare a wajan ba ita kanta Mariya bata so yin taron ba bayar da za tayi ne Baseera son bidi'a gareta sannan ta samu goyan bayan su Dr.Karami. Haka ko waccen su ta koma gida a gajiya Mariya gabadaya ta gama yin la'asar musamman in ta tuna gobe kamar yanzu ta jima da zama matar wani abin sosai take jin sa wani iri banbarakwai a cikin wannan daren sai da Umma ta kara kwantar mata da hankali sannan ta kara nuna mata darajar aure da martabobinsa ga 'ya mace sanna ta tunatar da ita fa'idar hakuri da juriya a gidan aure da duk wasu tsarurruka da yakamata ta bi domin dacewa da gidan aurenta sosai ta tsoratar da ita akan raina miji da dangin sa sosai ta nuna mata illar kin biyayya ga miji da duk wasu abubuwa da za su bata mata gidan aure ta. Gyaɗa kai kawai Mariya take yi tana jin yarda zuciyarta ke kara tsinkewa da lamarin a wannan daren barci sai dai barawo ne ya yi yawon gaba da ita... *Kamala Minna*😘😘😘😘 [11/2, 8:27 AM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU BALA'I NA. KAMALA MINNA. *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA SABA'IN DA DAYA. Zazzaɓi ne mai zafi rufe ta, bata tare da kowa ya sanin ba, sai karkarwa take yi numfashinta na kai wa da kamo wa, sautin haduwar hakoranta sai bada sauti yake yi gabadaya ta jigata, cikin wani irin yanayin tun a daren jiya. sosai take jin jikinta ba dadi, sosai take jin kamar akwai abin da ke shirin faruwa da ita, motsin da taji na shigowa ne ya sanyata kara kankame jikinta, zama taji anyi kusa da ita gami da yaye bargon da ta lulluba dashi, kara runtse idanuwanta tayi. "Mariya". Taji sautin muryar Umma ta sauka a saitin kunnuwanta, numfashi taja kafun ta buɗe idanuwan nata a hankali, ta sauke su a saitin Umma. "Me ke damun ki haka Mariya, sosai naji zazzaɓi a jikinki, me yasa haka mai yasa kike son cutar da kan ki ne, bayan kuma kin san wannan abin ba abin cutar bane gareki, mu ma iyayenki mun sani ba za mu so abin da zai cutar dake a duniyar nan ba". Ta karashe cikin sanyin muryar tana riko kafadunta, ta tayar da ita zaune, tana dubanta. "Ban son haka Mariya, ya kamata ki ajje komai na fargaba da ke a zuciyarki duk wani bahagon zance da zaki ji zuciyarki da kwanyarki na kawo miki ki ajje su gefe, shaiɗan ne kawai ke miki kuwwa yaka so ya bata miki lamarin ki na alheri, ki kokarta ki mike lokaci tafiya yake yi nan da wasu awanni MATAR WANI zaki zama, karkashin wani zaki koma komai naki zai koma garesa, rayuwar taki ma kacokan zata bar hannunmu, mu iyayenki zata koma karkashin sa. kin ga kuwa bai kamata ki saka wa zuciyarki wata damuwa ba zama ne muke fatan har gaban abada ayi shi, zama ne mai daraja da martaba da kuma hanyar tsira gareki da mu kanmu iyayenki, Mariya ina horar dake ki rike darajarki da ta mijinki ki anshe shi a matsayin miji na tabbara Hisham ba zai taba cutar dake ba, duk da dai ansan DAN ADAM ajizi ne amma bana SHAKKA akan sa, ke ma na san ba za a taba samun matsala ta fannin ki ba". Hayaniyar da ta kaure ne a tsakar gidan ya sanya Umma saurin mikewa ta fice, yan biki ne suka cika tsakar gidan, ga wasu tika-tikan tukwane da aka daura an banka masu wuta ko wani bangare ka duba na cikin gidan, zaka gane eh biki ne na musamman za ayi sa na masu rangwamin rufin asiri. Haka abubuwa su kai ta tafiya, har misalin sha biyu da rabi, da yake daurin auren karfe daya ne nan da nan maza masu zuwa daurin aure suka fara shiri, amarya kuwa na can kudundune acikin daki, gabanta sai dukan uku-uku yake yi. Zaune take tana faman rarraba idanu tana duban jikinta yarda ya canza lokaci guda yayi haske gami da laushi, ga wani kamshi da yake ta fesowa daga jikin nata lokaci-lokaci take dago hannayenta tana kallo zane suke da lafiyayyan lalle baki da ja hakan ya kara ƙawata hannun nata sosai da sosai... Wayar Umma ce ta dau kara, da sauri ta dube gefenta in da take ajje, sunan da ta gani a jikin wayar ne ya tsinkar mata da gaba, runtse idanu tayi zuciyarta na mikata wani mataki mai girman gaske tana jin yarda zuciyarta ke kara buɗewa da wani al'amari mai girma a gareta, sosai take jin wani shauƙi da begen Dr.Karami na kara bula mata jikinta ta ko ina, burinta da fatan ta za su cika muraɗin zuciyarta yau zai kasance tabbatacce. A hankali ta kai hannunta ta dauki wayar gami da kaiwa kunnanta bayan ta latsa madannin ansa kira. Wani numfashi mai sauti ta ji ya ajje, kafun ya saki wani murmushi da taji shi har kunnuwanta runtse idanu tayi, tana buɗe su sosai. "Me yasa haka Mariya. kin san dai a irin wadannan lokutan sosai nake bukatar ki kusa dani ko na ji muryarki, amma tun jiya nake kiran wayar nan kin ki dagawa kin san kuwa yarda nake ji a raina, kin san kuwa irin damuwar da na shiga jiya zuwa wannan lokaci, ji nake yi kamar bani ba, zuciyata nake ji kamar ba ta kirjina kwata-kwata...". Da sauri ta zare wayar daga kunnuwanta tana duban fuskar wayar, don tabbatar da wanda take waya dashi. jin abin take yi kamar a mafarki, gani take yi kamar ba Dr.Karamin da ta sani ba, sautin kalaman take ji suna ansawa a cikin kunnuwanta da zuciyarta suna haifar mata da kasala. "kice wani abu mana Mariya Please, kin ganni nan yanzu haka na kasa shiryawa saboda rashin jin ki ko barci banyi ba jiya, sosai nake ji a jikina kamar akwai abin dake faruwa dake". Numfashi ta ja lokacin da ta mai da wayar kunnuwanta, tana jin yarda yake furucin nasa mai kokarin rikita mata lissafi, muryar take ji kamar batasa ba, muryar take ji ta sauya mata... "Please ki ce wani abu da zai karamin karfin guiwa mana, na kasa shiryawa, kin ga Dr.Aqeel har ya gama shiryawa tun dazu yake kirana a waya, suna hanya amma ni nakasa aikata komai Mariya sosai nake jin wani iri a jikina, sosai nake jin kamar akwai abin da zai faru..." Runtse idanu tayi gabanta yayi wani irin dokawa, mikewa tayi kan kafafuwanta kafunta ja numfashi mai tsayi. "Nima haka nake ji a jikina, ban san dalili ba". Ta fadi da wata irin murya mai taushi, wacce bata san tana da irinta ba. "Yaa Rabbi!!". Ya furta da sauti, kafun ya saki muryarsa sosai. "Dafatan dai ba wani abu bane yake damun ki ba, Mariya Please fada min abin da ke damun ki...ko da yake bari na zo yanzu kin ji...". "A,a ba sai kazo ba, ba komai Allah..". Ina! tun kafin ta ida zancenta har ya kashe wayar, sosai taji jikinta yayi sanyi komawa tayi ta zauna ragwaf! tana mai da numfashi bata san abin da ke damunta ba, gabadaya take jin wani iri a jikinta, kamar bata da lafiya. Sallamar da akayi ne ya katse mata hanzari, wasu mataye guda biyu suka shigo fuskarsu kunshe da murmushi suka isa gareta kallo daya tayi musu ta gane su waye, itama murmushin yaƙe tayi musu kafun ta hadiye abin da take ji ya tsaya mata a makoshi. "Ya kamata ki tashi ki yi wanka fa, lokaci tafiya yake yi kin ga har su Baffa sun wuce wajan daurin auren". Wani irin bugu taji gabanta yayi runtse idanu tayi, kafun ta buɗe su a saitin su, tana duban su daya bayan daya, wannan rana sosai take jin ta tana haifar mata da wani yanayi a zuciyarta, da ma jiki baki daya. komai take jin yana sauya mata komai na duniyar take ji yana canzawa. "Yaa Mariya..Yaa Mariya". Mu'azzam ne ya shigo da gudu har yana kokarin faduwa, Mariya ta kai hannu ta riko shi tana dubansa. "Kizo wai inji...". Da sauri ta rufe masa baki, tana ajje numfashi. a zuciyarta ta shiga mamaki da tu'ajibi akan zuwan Dr.Karami, don ta tabbata shi ne ba wani ba. tana mamakin sa cikin yan kwanakinnan musamman irin kulawa da yake bata, numfashi ta ja kafun ta dubi su Asiya da suka zuba mata idanu, kau da kai tayi yarda zata fita ne take tunani ta tabbata ba za a bar ta ba, amma zuciyarta sai tunzurata take yi akan ta fita taje domin kuwa ita akaran kanta tana son ganin sa. Mikewa tayi ta ja hannu Mu'azzam sukayi tsakar gida, su dai su Asiya ba su ce mata komai ba, sai bin ta suke da kallo, ba su gano abin dake faruwa ba. A hankali suka karasa tsakiyar tsakar gidan hankalin yan biki duk yana wajan aikin da suke, kara sauko da gyalen jikinta tayi, ya rufe mata fuska sosai, sai da ta tabbatar ba Umma a wajan da sauri ta fada soro sannan suka tsaya ta dubi Mu'azzam. "Dr.Karami ne?". Gyaɗa kai yayi. Batare da ta sake cewa dashi komai ba, suka nufi waje can ta hango shi jikin motarsa, jikinsa sanye da riga da wando kananu wani haske taga ya kara yi mata gami da kwarjini kau da kan ta tayi, zuciyarta na mikata matakin son Dr.karami da take jin yana kara narkar da zuciyarta. Sam bai lura da su ba sai da ya dago kansa daga wayar da ake ta faman kiransa ya kasa dagawa, da sauri ya shiga takowa garesu ji yake yi kamar fizgarsa ake yi idanuwansa gabadaya suna kan Mariya ya kasa dauke su, har ya iso inda take tsaye bai sani ba numfashi ya ja lokacin da yaji wani kamshi mai ratsa zuciya na dukan hancin sa, idanu sosai ya zuba mata kafun ya shafi fuskarsa. "Me ke faruwa ne?". "Ba komai". Ta bashi ansa a daidai lokacin wayarsa ta sake daukar burari da sauri suka dubeta su duka, sunan kawunsa ya gani da sauri ya daga, ba tare da yace komai ba na yan sakanni ya numfasa. "Ga ni nan zuwa Kawu, ina kan hanya yanzu haka kayi hakuri". Ya fadi yana sauke wayar, idanu ta kura masa kafun ta ce. "Sai da nace karka zo, don Allah ka tafi na san suna can suna jiranka". Tana gama fadin haka ta juya cikin gida da sauri, tana jin yana kiranta amma ko ta kan sa ba ta bi ba, saboda yanayin da take jin dukan zuciyarta. ***** Misalin karfe daya da mintina ashirin aka shaida daurin auren DR.HISHAM MUKHTAR KARAMI da MARIYA BELLO GWADA sannan na DR.AQEEL MUNKA'IL da BASEERA HARUNA SA'AD daga karshe aka daura na HAFSAT DANLITI da HUZAIF ABDURRAZAQ sosai babbar masallacin juma'an garin Gwada ya cika, sai kace ranar idi gabadaya ma garin in ka shiga zaka gane ana gagarumin biki, Angwaye biyu bakin su a buɗe cike da farin ciki da muraɗan jindadi, haka yan uwa da abokanan arzuki, sai dai Ango daya in ka kalle shi kamar bakin kumurci haka ya koma, domin ana gama daurin auren ya bar wajan zuciyarsa yake ji tana zafi da raɗaɗi bai so zuwa ba kawai don ba yarda ya iya ne huzaif wannan ranar ta kasance masa ta bakin cikida takaici a filin duniyarsa, bai taba zaton abin zai tabbata ba sai yau, sosai yayi kudiri a zuciyarsa sai ya baiwa Hafsat mamaki sai ta gwammace zaman gidan yari da gidansa, sai ya gana mata azabar da sai tafi kaunar mutuwar da ita. Misalin karfe biyar na yamma aka shirya hadaddiyar Dinner a Hdyro hotel dake cikin Birnin Minna, sosai liyafan ta hadu waje ya cika makil amare da angwaye sun sha kyau na musamman kowa ka gani fuskarsa kunshe da farin ciki da jin dadi. Misalin karfe tara aka tashi ko wacce amarya da ta wagarta suka nufi gidan su, zuwa lokacin Mariya ta gama sadakarwar komai ya tabbata, ta zama matar Dr.karami sosai take jin zuciyarta na buɗewa tana kara haifar mata da son sa, komai take ji nata na duniya ta mika masa. Lokaci lokaci take dauke hawayen da suke kwaranyo mata musamman in ta tuna rayuwarta a can baya, yarda ta kasance wai yau ita ce a wannan mataki ikon Allah kenan. Ko da suka koma gida nasiha sosai akayi musu mai ratsa jiki da zuciyar duk wani wanda yake zaune a wajan, Mariya kuka take yi mara sauti tana jin yarda a yau za ta rabu da Ummanta, zata rabu da Abban ta da Mu'azzam din ta, lokaci guda ta tuna lokacin da Dr.Karami yake cewa da ita anya zata iya rabu da Mu'azzam yarda take nuna masa so da kulawa?. Tabbas yau ga ranar ta zo ranar da zata koma wani gida na daban, gidan da Umma tayi mata fatan zama na har abada. A banagaren Hafsat kuwa rigima ce ta kaure sosai domin suna zuwa gidan amarya suka tadda su Assama'u sun kasa sun tsare tun daga lokacin da Hafsat ta sako kafar cikin gidan bayan an gama artabu wajan daukota don sai da akayi dak'yar sannan aka aiko da mota daya abin ya kara tayar mata da hankali ganin irin luntsuma luntsumar motocin da aka zo daukar Mariya da su sun yi jejir gwano a kofar gida hakan ya kara tabbatar mata da cewa Huzaif da gaske bai kaunarta. Numfashi ta ja wasu hawaye su zubo mata a kunci zuciyarta take ji tana sanar da ita irin kalubalan da zata fuskatan tun a yanzu a daren farkonta an fara yi mata rashin mutunci da wulakanta wanda suka kawo ta ina ga kuma an barta ita kadai ta san Huzaif da su Assama'u romanta ne kawai kila ba za su sha ba... *Kamala Minna*💞💞😘😘😘 [11/2, 8:27 AM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU BALA'I NA. KAMALA MINNA. *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA SABA'IN DA BIYU. *BAYAN WANI LOKACI...* Sosai take kuka ta mike kan kafafuwanta gabadaya take jin jikinta wani iri, ga wani zafi da radadi dake jinsa a duk wata gaɓa ta jikinta nayi mata, bata taba zaton muguntar Huzaif ta kai haka ba, bata taba zaton rashin imanin nasa ya kai haka ba, ta yi zaton zaman na nasu zai sauya tayi zaton zasu fahimci juna, ashe ba haka bane duk inda take zaton Huzaif ya shalle tunaninta da nazarinta. A hankali ta shiga dafa bango tana jan kafafuwanta har ta isa kofar toilet ta buɗe ta shiga, zuciyarta take ji tana kuna da suya ji take yi kamar zuciyar zata faso son sa na nan har yanzu ba abin da ya ragu, sai ma kara buɗewa da zuciyarta take yi da son sa. Ruwa mai dumi ta cika kwarmin wanka da shi sannan ta shiga sosai zafin ke ratsata ta ko ina, sosai take jin zafin na kaiwa duk wani sashi da gurbi da take jin yana ansawa. Runtse idanu tayi lokaci guda ta buɗe, sosai take jin rashin nadama akan son Huzaif alkawari tayi ko da yana yankar naman jikinta zata zauna dashi har karshen numfashinta, ta gwamma ce ta ji azabar gidan miji da dai ta koma waccan bakin gidan na Goggo Marka, ta koyi rayuwa tun daga irin cin zarafi da cin mutunci da gori da ta ake mata a wannan gidan ta tabbata in ba tayi wasa ba su Assama'u so suke su fidda ita, amma zata jajirce zata nemi gafarar Allah ya yafe mata laifukanta ta sani abubuwan da ta aikata ne yake bibiyarta ba komai ba a duniyar rayuwarta. Ta jima kafun ta tsane jikinta ta fito sam ba ta lura da mutum dake tsaye bakin kofa ba yana ta faman sakar mata wani irin kallo, sai da ta zauna bakin gadonta sannan ta lura dashi gabanta taji ya yanke ya fadi runtse idanu tayi tana tuna artabun da suka kwasa a jiya zuwa yau, goshin sa ta kalla kinkimeman bandeji ta gani runtse idanu tayi tana tuna fadawa da Huzaif yayi jikin Mirrow ya fasa masa goshi, sosai ya yanke shi don jiya ta ga ta shin hankali bata taba zaton Huzaif zai rayuwa ba, musamman irin jinin da ta ga ya zubar da irin sambatun da yake yi. A hankali ya shiga takowa ya iso gareta gefenta ya zauna fuskarta da wani irin yanayi mai cike da alamun nadama idanuwansa sun kada sunyi jajir gabanta ne ya yanke ya fadi sosai take kokwanto akan abin take hangowa cikin idanuwansa tausayi abin ya bata mamaki. ***** Hajiya Layla ce ta dubi Khairiyya dake zaune ta zabga tagumi LAMARIN DUNIYA gabadaya ya kara hargitsa mata lissafi, komai na duniyar take jin sa wani iri babu dadi, duk da a yanzu bata da wata matsala a rayuwarta wacce zata addabeta amma in ta tuna wacece ita sai taji zuciyarta na kuna gami da suya, hawaye suka zirnano mata a hankali ta dauke su tana ajiyar zuciya. "Khairiyya!". Hajiya Layla ta fadi da sauti a muryarta mai cike da rarrashi da karfafa mata gwiwa akan lamarin rayuwar da suke ciki a yanzu, kusa da ita ta karasa tana toshe bakinta jin tari na kokarin sarke ta, a hankali ta zauna tana mai yatsine fuska alamun akwai abin da ke damunta na rashin jindadi. "Haba mana Khairiyya. bana so nake ganin ki cikin wannan yanayin gabadaya sai naji babu dadi, na rokeki ki mai da komai ba komai ba duba za kiyi da baya da irin rayuwar da mu kasance da kuma yanzu, ai abubuwa sun yi sauki kuma kisan ita rayuwa ba ko yaushe take zama daidai ba, kuma ba wani bawa a doron duniyar nan da zai ce miki ya dawwama a farinciki da kwanciyar hankali a rayuwa kowa da yarda Allah ya ke kunsa masa matsalarsa, sai dai ace ta wani bawan tafi ta wani". Ta karashe tarin na kara sarke ta, da sauri Khairiyya ta dube ta cikin yanayi na tausayawa. "Maama kin sha maganinki kuwa?". Gyaɗa mata kai tayi gami da sakin murmushi kafun ta dafa kafaɗarta. "Khairiyya Ina son mu sake zama na biyu dake, kuma ina so wannan zaman ya zama na karshe tsakanina dake, sannan ki sani ba zan tursasaki ba sannan ba zan yi miki dole b,a ni dai fata na kawai ki samu kwanciyar hankali ako ina kike shine BURINA sannan shi abin da na fi bukata a duniyar nan, Khairiyya so nake yi na zama sanadi na wanzuwar farin cikin ki har kashen numfashinmu a doron duniyar nan...". "Maamaa". Khairiyya ta fadi da alamun rigima a muryarta, kafun ta juyo sosai ta fuskance ta tana bayyana wani kunshin murmushi, wanda ta san zai kara kwantarwa Hajiya Layla da hankali. "Ina jin ki faɗa mani menene zan anshe shi a duk yarda ya zo mani, zan yi AMANNA dashi BURINA a duniyar nan shine na faranta miki, kullum na ganki cikin farin ciki Maama kece farincikina kece komai a rayuwata kece kika zama tsanin ganin rayuwata ta gyaru...". Hawaye ne suka kwanranyo mata da sauri ta kau da kanta, tana jin yarda zuciyarta ke kara buɗewa farinciki na kara samun gurbi a cikinta. "Maganar Alhaji Abdulwahaab Khairiyya ina muka kwana?". Ta fadi tana saka idanuwanta cikin na Khairiyya, so take yi ta hango gaskiya, so take yi ta gano in da Khairiyyar ta dosa da batun, so take yi ta ga yanayin ta ko na sauyi a yarda ta dauki maganar a yanzu. Numfashi taja gami da fesarwa kafun ta mike kan kafafuwanta, zuciyarta take ji tana kara buɗewa kaunar da Hajiya Layla take nuna mata bata san da mai zata saka mata ba, ta nuna mata so ta nuna mata kauna tayi tattalinta ta bata duk wani lokacinta, sannan ta bata farincikin daidai iyawarta ya kamata ita ma ta nuna mata godiyarta sannan ta anshi duk wani abu da ta zo dashi, hakan zai kara tabbatar wa Hajiya Layla da cewa sun zama UWA DA 'YA. "Maama na lura dai so kike yi ki samu suruki". Ta fadi fuskarta da murmushi ita ma Hajiya Layla murmushi take yi kafun ta mike tana faɗar. "Ba suruki kadai ba har da jikokina nake so na gani, kafun lokacina yayi so nake yi ni dake ki saman mana DANGI da zuri'a, zan yi alfahari da hakan sannan ko na mutu zan san nima ina da dangi". Ta karashe da kwalla a idanuwanta. "ki anshe shi a matsayin miji na san Alhaji Abdulwahaab zai rike ki a yarda kike zai kula min dake, zai tattale ki zai zama MIJIN MARAINIYA a gareki, na san ba zaki taba kokawa ba duk da dai an san DAN ADAM ajizi ne, amma a zuciyata fata nake ke da Alhaji Abdulwahaab ku zamo abu daya har a gidan aljanna". "Shikenan Maama nifa wannan kukan naki ne bana so, Allah ki dai batun Alhaji Abdulwahaab kuma ai tuni labari ya sauya kawai fadi miki ne ban yi ba". Zaro idanu Hajiya Layla tayi cikin alamun mamaki, kafun ta kai wa Khairiyya dukan wasa ta goce. "Ja'ira dama kallona kawai kike yi, ina kidina ina rawa ta ko? Allah ya shirya min ke ni nan na saki baki ina cewa sai na hada miki da tsayuwar dare ayi auren nan, ashe tuni kin mai dani wata kakarki to ai shikenan Allah yasa hakan shine yafi zama alheri a garemu ga baki daya, Allah yasa fatan da muke ya tabbata Allah ya kau da duk wata fitina da abin ki Allah ya kare miki rayuwa 'yata Allah ya kawo zuri'a tagari kiyi ta haifar mani tagwaye". Ta karashe tana goge hawayen da suke zubo mata ta jawo Khairiyya jikinta ta rungumeta sosai suke jin wata natsuwa da kwanciyar hankali na wanzuwa garesu. "Ameen Yaa Rabbi Maama na". Khairiyya ta ansa muryarta na rawa. ****** Da Sallama ya shigo cikin gidan, yana bin duk wata kusurwa da kallo yarda gidan ya dawo tsaf! komai ya zama sabo zuciyarsa yake ji tana kara buɗewa da farinciki gami da kwanciyar hankali, ba abin da zai ce sai godiya ga Allah da kuma Dr.Karami da ya zama sanadin samun waraka a rayuwarsu duban jikinsa yayi kafun ya sake duban gidan kwalla suka tarun masa kafun ya dauke su, a hankali ya shiga takawa yana isa dakin Umma, daga labulan yayi bakin sa da Sallama. Zaune take gabanta da katuwar roba mai cike da CAKE tana lissafawa jin sallamar maigidan ne ya sanyata tsagaitawa, ta ansa sallama tana kokarin mikewa ta anso kayan hannunsa ya iso da sauri yana fadin. "Matar nan kin zama Hajiya fa Kasuwancin nan ya anshe ki sosai kin yiwa 'yata wayo ita da koya ke da karbe sana'ar". Murmushi tayi kafun tace. "Yo da zaman banza ai gwanda aiki kishiya kuma ai bani nace ta bar mani ba kuma ko ma kace na anshe mata ai ba gida daya muke ba ita za ta iyayin nata a gidan auren ta kowa ya ci da rabon sa". Zama yayi yana mai fadin. "To Allah ya dafa mana kin ga na shagon ma da kika kai shekaran jiya kusan karewa na lura Cake din nan yana karbuwa sosai wajan jama'a da mutum yaji cikin sa yana masa yaƙi sai ya zo ya hada da lemo sai ki ga ya dawo hayyacinsa". Murmushi tayi batare da ta kara cewa komai ba, amma zuciyarta tana goɗewa Allah tana shiwa Dr.Karami Albarka yarda ya fiddo dasu daga cikin kangin rayuwa ya baiwa mijinta jali ya buɗe shagon kayan bukata na rayuwa gashi ita ma sanadin karatun 'yarta ta samu sana'ar yi ba abin da zata cewa Allah sai godiya da fatan karin kwanciyar hankali daga gareshi. "Wai ina karya jali yake ne?". Ya tambaya yana murmushi, dubansa tayi. "Au kai ma Mariya ta bar maka sara ko ɗan nawa ne karya jali ai yanzu na uwarsa ne ko ya karya ba damuwa wata rana shi zai daura...yana can ya tafi Islamiyya". Dakin ne ya dau shiru na dan lokaci, kafun Bello ya ja dogon numfashi ya dubi Umma. "kisan mi ina labarin yan matan nan da nace miki mun hadu da su wajan mutanan nan da suke garkuwa da mutane?". Umma ta gyaɗa kai tana gyara zamanta ya cigaba da fadin. "Yanzu a shagon Alhaji Adamu mai bulawus na gan su an nuna a talabjin ashe lokacin da na bar su tana da juna biyu shugaban tawagar na su shi yayi mata a cikin sauran yan matan ma akwai masu juna biyu duk sun haihuwa yau na ga shari'ar da aka yi musu yau aka yanke musu zaman gidan kaso na rai da rai duk kan su su kuma yan matan gwamnati ta dauki nauyin rayuwarsu saboda kin san garin na su an kone duka sannan duk an kashe iyayen su ba su da kowa ba su da komai yanzu naji tausayin su sosai". Umma ta dauke hawayen da suka zubo mata domin ta jima tana tuna wannan labarin na mutanan da suka kama mata miji sannan da yan matan da ya bata labari akan su. "Allah ya sa iyakar wahalar rayuwarsu kenan Allah ya jibanci lamarin su su kuma wadannan mutane Allah yayi mana tsari da irin su ya kare mana rayuwa da ta yan uwanmu daga fadawa hannun su". "Ameen Ya Rabbi". Ya ansa jiki a sanyaye yana mikewa. "Ka duba Jin Goggo fa don Allah Malam bai kamata ace kana mata haka ba, ita ma uwa ce a gareka duk wani abu da tayi maka na cutarwa ina rokon Alfarma ka yafe mata, rayuwar duniyar nan ba komai bane...". "Naji kuma ai ni tuni na yafe mata, kowa dai yayi na gari dan kan sa". "Malam don Allah ka manta komai a rayuwarka da tayi maka, ita ma ai tayi nadama ko halin da take a ciki yanzu yaci ace ka tausaya mata". Bai sake fadin komai ba ya fice daga cikin dakin, tsayawa yayi yana kallon dakin Goggo Marka kamar ba zai je ba, sai kuma ya taka a hankali ya isa kofar dakin daga labule yayi can karshen gado ya hangota gabadaya ta gama yankwanewa idanuwanta a buɗe tarwai sai dai ba su da amfanin komai kusan watanni hudu kenan cutar MAKANTA ta lokaci guda ta kama ta tun da akayi wata iska kura ta shigar mata idanu shikenan ta makance kuma dama gashi tana faman da cutar hawan jini da tayi mata mugun kamu har ta kashe mata ɓarin jiki tashima bata iyayi daga kwanciya sai kwanciya... *Kamala Minna*😘😘😘 [11/2, 11:56 AM] DEENY MINNA🙋‍♂: UKU BALA'I NA. KAMALA MINNA. *ZAMANI WRITERS ASSOCIATION* ​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​. BABI NA SABA'IN DA UKU *MARUFI...* "Mai Ciki". Kamar daga sama taji sautin muryar Bassera na fadin haka, cikin dariya a hankali ta mike tana gyara doguwar rigar dake jikinta, ta taka hankali ta nufi kofar fuskar da murmushi, Handle din ta rike gami da buɗewa. Baseera ce tsaye, hannunta sarke da na Dr.Aqeel hankalinsa gabadaya na wajan wayar da yake yi sai ɗan ta TAUFEEQ dake sagale a kafaɗar Dr.Aqeel din. Numfashi Mariya ta ja kafun ta zaro idanu waje, da sauri ta koma ciki tana mai kwalawa Dr.karami kira, da yake kicin. Wai yana yi mata wainar fulawa tunda ta tashi take kwadayinta shi kuwa ya zage sai yayi bayan kuma tace zata aikawa Umma tayi mata, yace bai amince ba shi ma ya iya. Da sauri ya fito idanuwansa sun yi jajir, hannunsa rike da cokali fuskar gefe guda duk Manja, bata san lokacin da ta kwashe da dariya ba ta shiga nuna masa kofar shigowa falon tana yi masa alama da baki amma ya kasa gane wa, sai ma harara da wurga mata yana fadin. "Ni ko ai ko ba za ki ci wainar nan ba tun da abin ya zama haka...". Bai karasa ba Baseera ta bayyana cikin falon, duban su tayi kafun ta sauke idanuwanta a saitin Dr.Ƙarami da yayi wiki-wiki dashi. "Iyee ba shakka, likita kai ne haka". Ta fadi tana kwashewa da dariya, a sa'ilin da Dr.Aqeel ya sanyo kai shima yana kokarin sauke TAUFEEQ a kafaɗarsa, ganin abin da ke faruwa ya sanya shi isa cikin falon da sauri ya kwantar da Taufeeq da ya yi barci ya zauna gami da zabga tagumi yana kallon Dr.Karami, kafun lokaci guda ya kwashe da dariya. "Aboki ashe kai ma kuku ka zama tabbas arzuki yaci uban na da, an sai da gida an sai yashi". Gabadayan su suka kwashe da dariya, kafun Dr.Karami ya juya da sauri ya fada kicin, yana tuntsirar dariya shima. "Billahillazi baki da M matar nan yanzu Doctor guda ya zama kukun ki". Baseera ta fadi tana duban Mariya, taɓe baki tayi tana mai cewa. "Dadin abin ai ba ni kadai ake yi wa wannan gatan ba na ga wata mike kafa take yi ta tura mijin nata kicin ya yi ta fama da cokali a hannunsa". "Rabu da ita Maman Jawwad yanzu haka kafun mu fito, nifa nayi girkin wai bata da lafiya ba yarda na iya haka na shiga na zabga girkin kuma saboda rashin tsoron Allah ta miki kafa ta buɗe ciki ta ci". Dr.Aqeel ya fadi yana marere cewa alamun ya ji jiki wani kallo Baseera tayi masa kafun ta ce dashi. "Au haka ma zaka ce? to shi kenan tun da kace haka da ga yau raba girki za mu din ga yi da kai, kowa ya din ga yin kwana bibbiyu". Zaro idanu yayi gami da daura hannu aka, kamar wanda ya ga wani mugun abu ya shiga marmaɗi da idanu kamar wanda yayi wa sarki karya. Baki Mariya ta saki ganin yarda yayi a daidai lokacin shi kuma Dr.Karami ya fito, hannunsa dauke da faranti shake da wainar fulawa taji manja ya iso gaban Mariya ya kalle ta sama da kasa kamshin wainar ta doki hancinta lokaci guda taji miyau dinta ya tsinke, da sauri ta kai hannu zata dauka ya kau ce yana yi mata gwalo gaban Dr.Aqeel ya isa ya zauna ya dube shi. "Wannan aikin maza, ne don haka zo mu ci a tsakaninmu, in sun yi zuciya suyi na su mugani". Ya fadi yana daukar waina daya ya kai bakin sa kafun ya mike ya nufi firji ya buɗe ya dauko musu gorar ruwa da ta lemo masu rangwamin sanyi. Baseera baki ta saki kafun ta dubi Mariya dake tsaye tana ta faman hadiye yawu, fuskarta duk tayi wani iri kamar zata fashe da kuka a hankali Baseera ta mike ta dube su. "Dadin abin mu ba kutare bane, sannan kuma muna da hannun da za muyi bari ma ku gani". Tana fadin haka ta mike ta nufi in da Mariya take sai faman hadiyar yawu take ta rike hannunta suka nufi Kicin. Da gudu Dr.Karami ya mike hannunsa da waina daya gaban su ya sha ya riko hannun Mariya gami da bude mata baki, ya tura mata wainar aiko kamar jira take ta shiga taunawa har tana kokarin kwarewa. Baya Baseera tayi tana kallon ikon Allah kafun ta juya ta dubi nata Mijin da ya dauke kai yana ta faman kai loma bakinsa. "IKON ALLAH" Abin da ta fadi kenan tana rike haɓa. ***** Karar faduwar abu ne ya sanyata fitowa daga kicin cikin sauri, sai faman jan kafa take yi da turtsetsen cikin ta tana cizon laɓɓanta daidai benen da zai kai ta sashinta kafarta ta turguɗe ta yo baya runtse idanu tayi don ta sadakar taje kasa har ta hango irin zabar da wahalar da zata sha jinta tayi jikin mutumin da bata taba zato ba, wani numfashi ta ajje a daidai lokacin da ya riko mata kugunta ya haɗe da jikinta sosai kamshin turaren sa Dark-wood wanda ya rigaya ya zama jikinsa ya daki hancinta hakan ya kara sanyata lafewa a jikinsa. Sun dau lokaci a haka kafun ya ja numfashi bayan ya gama shinshinar kamshin da ke fita daga cikin sumar kanta da ta sha gyara ta tufketa da rumbos. "Kashe ni zaki yi ko Preety?". Ya fadi yana mai dago haɓarta da hannu daya, idanuwanta a runtse suke har zuwa wannan lokacin taki buɗe su ita kadai ta san yanayin da take ciki a wannan mataki, zuciyarta take ji tana mikata wata duniya ta daban mai cike da farin ciki na tsanani kaunar da take ji zuciyarta na kara narkewa ta mijin nata abin alfaharinta. Iska ya shiga hura mata a idanu ta shiga motsa manyan kwayan idanuwanta ba tare da ta buɗe ba, wani murmushi na kara bayyana a saman ƙyankyawar fuskarta wacce tayi fayau ba digon ko tabo a jikinta laɓɓanta masu taushi da kalar ja sai faman motsa su take yi a hankali ta shiga buɗe idanuwanta daya bayan daya ta sauke su a saitin fuskarsa. "Jawwad!". Ta fadi da wani irin sauti a muryarta kafun ta shiga kokarin mikewa daga lallausar jikin nasa da bata gajiya da kwanciya a kanshi kirjinsa da ya zame mata abin kwanciya a kullum in ba a nan ta kwanta ba ta taba jin dadi sannan ba ta iya barci. "Me ya yi kuma?". Ba tace komai ba ta mike daga jikin nasa gabadaya ta kwace kanta daga rikon da yayi wa kugunta a hankali ta shiga takawa tana kokarin hawa sama amma jin yarda kugunta ya ansa ya sanyata tsayawa cak! tana mai cizon laɓɓanta. "wash!!!". Da hanzari ya riko ta, yana mai duban inda ta rike. "Ya dai me ke damun ki haka?". Turo bakin tayi gaba gami da taba kugun nata da take jin sa kamar zai karye. "Shiyasa nace maki ki dawo dakin kasa da zama amma kin ki wannan benen so yake yi ya karya min bayan mata wallahi". Kafin ta ce wani abu caraf! ya sungume ta kamar wata Baby ya hadata da jikinsa sosai ita kuwa ta shiga kiciniyar kwace kanta amma ina rikon da yayi mata ba na wasa bane hakan yasanyata yin lamo a bayansa tana cizan masa kunne har suka isa dakinta da sauri tace dashi. "Don Allah sauke ni Jawwad yana ciki fa!". "Ai baki isa ba wallahi sai na kai ki har ciki sannan na rama cizo na da kikayi mani". Jin abin ya yace ya sanyata marere cewa tana shagwaɓe baki alamun son yi kuka hakan da yaji da sauri ya sauke ta yana riko hannunta. "Ai wallahi sai na rama haka kawai so kike yi ki rage mani farashi budurwa tace bata so na ko". Zaro idanu tayi waje tana dubansa gabanta taji ya yanke ya fadi kafun ta tako kusa dashi tana zira idanuwanta cikin nasa. "Me kake cewa wacece gangancin da neman ciwon zuciya take so ta zama MATAR MIJINA a garin nan?". Yanayin da ta nuna yayi matukar bashi mamaki bai hango wani razana ko tsoro a idanuwanta ba amma ya hango tsantsar so da kuma kishi na asali a cikin idanuwan nata. "Abin da kika ji shi na fadi". Ya karashe yana rike Handle din kofar ya tura yana kokarin shiga ciki da sauri ta sha gabansa tana sake saka idanuwanta cikin nasa. "Ban hango akasin gaskiya a idanuwanka ba bai kamata kake barin harshen ka na kokarin fadin abin da ba daidai ba". "Injiwa ya fada miki ba gaskiya nake fadi ba ai kina sauke mani TAGWAYE na zan dakaro miki sabuwar amarya fil a leda". Zaro idanu tayi kafun ta mai da kallonta zuwa cikinta ta shiga shafawa. "Tagwaye fa kace ni gaskiya a,a cikina guda daya ne kacal zan haifa ba wani tagwaye". "Au! Wasa kika dauka to ai shikenan Allah ya kamu lokacin zaki ce na fada miki". Ya karashe da dariya sosai a fuskarsa ya fada cikin dakin, sake da baki ya barta tana bin sa da kallo, sannan ta bin cikin nata da yayi katoto ba kamar cikin Jawwad ba gyaɗa kai ta shiga yi, a zuciyarta tana jin kamar maganar Dr.Karami gaskiya gabanta taji ya yanke ya fadi ba abin da ta tuna sai lokacin haihuwar Jawwad yarda aka sha artabu. Wata dariya ce ta zo mata lokaci guda ta saketa da gudu ta fada cikin dakin duban Dr.Karami tayi da ya baje a gadonta can gefe kuma Jawwad ne da kwalbar Humra din ta da ya tarwatsa ta da sauri ta isa gareshi yana ganinta ya mike yana shirin gudu ta riko shi sannan ta dubi Humra din da ta kwarare a tsakar dakin sannan ta dubi Dr.Karami kara ta saki a razane ya tashi yana dubanta wani kallo ta watsa masa kafun ta turo baki gaba tana nuna masa Humra din ta dariya yayi kafun ya dubi Jawwad da yayi tsuru-tsuru. "Ni fa ba ruwana ke da ɗanki ne jiya nan yayi mani barna zan dake shi kika hanani don haka sai ke kiji in dadi". Jin abin da yace yana kunshewa dariya hakan ya sanyata duban Jawwad ta talla ke masa keya ta shiga dire-dire da kafafu tana shagwaɓe fuska alamun son yin kuka. Da sauri ya taso ya iso gareta ya kamota ya hadata da jikinsa sosai ya sanya bakinsa saitin kunnanta yana yi mata raɗa fizge kanta tayi ta tureshi bai ankara ba yaji ya faɗa kan gadon bin shi tayi tana kokarin turmushe shi yayi sauri matsawa gabadaya ta fada kan gadon binta yayi ya danne yana mai yi mata cakulkuli dariya ta shiga yi sai da yayi mata lilis da jiki sannan ya daga ta idanuwanta a rufe sai mai da numfashi take yi kiss ya manna mata a kumatu kafun ya riko hannunta ya shiga kallonta zuciyarsa na kara buɗewa sosai a son ta GURBIN SO da ya bata a duk wani fanni na zuciyarsa yake ji yana kara buɗewa da kaunarta kaunar da har abada ba ya tunanin zai iya yiwa wata ƴa mace a filin duniyar nan. "INA KAUNAR KI". Ya furta da wata irin murya da ta galabaitar da zuciyar Mariya a lokaci guda ji take yi zuciyarta na mikata wani waje na musamman mai tatttare da so da kauna zalla ta Dr Karamin ta sosai take jin zuciyar na kara buɗewa da kaunarsa sosai take jin duk bugun numfashinta na kara haifar da sabuwar kaunarsa a zuciyarta. "INA KAUNAR KA". Ita ma ta fadi da wata murya da ta daki kunnuwansa runtse idanu yayi yana jin yarda bugun zuciyarsa ke karuwa saitinta yaje ya kwanta yana jawota cikinta sosai ya matse ta har sai da ta saki ƴar kara ta buɗe idanuwanta. "Dady kai ko". Kamar daga sama suka jiyo muryar Jawwad na fadin haka da sauri suka dube shi don sun manta ma dashi a wajan gwalo Dr.karami yayi masa kafun ya mika masa hannu alamun ya taho da sauri yaje maimakon yaje wajan sa sai ya nufi wajan Mariya da sauri yana faɗawa jikinta. Dukkansu ya hada ya matse a jikinsa yana furtawa Mariya kalamai zafafa da suka kara tabbatar mata da Dr.karami na tane ita kadai har gaban abada. KARSHE!!!. ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH!! ALHAMDULILLAH!!! Godiya ga Allah da ya bani ikon kammala labarin na ina godiya sosai ga maso wannan labarin da su ta jimirin bibiyata har zuwa wannan lokaci ina godiya Ina neman afuwanku ga dukkan wani makaranci da na batawa rai da wanda na sani da wanda ban sani ba ku sani dan adam ajizi ne. Ku masoya ne ba na tunanin zan yi abu da gangan don na bata muku ku ajje haka a ranku Yau dai mun sauke labarin Uku bala'i Shin wani darasi kuka dauka a labarin nan? Mai ya bata muku rai a cikinsa? Me yafi faranta muku cikinsa? Wani jarumai ne suka fi burge ku sannan wanne su ka bata muku rai? Tsakanin jaruman nan me za ku iya cewa a ko wani dayan su Kalma akan Mariya Kalma akan Baseera Kalma akan Dr.Ƙarami Kalma akan Dr.Aqeel Kalma akan Hafsat Kalma akan Goggo Marka Kalma akan Areefa Kalma akan Hajiya Layla Kalma akan Dr.Erena Dss Shawara ko gyara Kofa abuɗe take Whatsapp 08076708191 Call 07039355645 Gmail.Kamalminna217@gmail.com Fatan alheri ga kowa da kowa ina son ku masoya sai mun hadu a sabon aiki a sabuwar shekara mai taken.....😁Sai kun ji...lolz