DOCUMENT MADE BY ESHAAT SMILER HOM OF HAUSA NOVLS DOCUMNTS WASAPP 08066360176 FOR MORE 鈥�: 漏 Fikra Writers Association *KASHE FITILA*馃挕1 *Batul Mamman*馃挅 *FWA Girls Secondary School Abuja* _SS 2A_ Hankalin malamin Civic Education da kusan duka daliban yana kan monita wadda aka sanya rarraba takardun test da akayi satin da ya wuce. Wannan ya bawa 'yan mata biyu cikin daliban da suke zaune a layin farko daga tsakiya damar karasa shirin abin da suke kullawa tun safe. Daya daga cikinsu ce ta rike ciki tare da kwalla kara iya karfinta sannan ta sulale a kasa ta kwanta. Kafin malamin da sauran su ankara dayar ta durkusa a gabanta tana jijjigata a hankali da muryar kuka take cewa "Rumana me ya sameki, tashi don Allah, wayyo...." Murmushi ne yaso kwacewa Rumana ai kuwa taji kyakkyawan mintsini daga wurin Yusra kawarta "don ubanki idan kika tona mana asiri wallahi cewa zanyi ba dani akayi ba" Tsabar tsoro ne yasa Yusra yin zagin. A lokacin malamin har ya iso, sauran 'yan aji duk an zagaye su ana tambayar me ya faru. Yusra harda kukanta tace haka kawai ta ga Rumanan ta fadi. Health prefect aka kirawo daga ajinsu tare da taimakon Yusra da wata malama suka kai Rumana karamin asibitin cikin makarantar. Sannan aka nemi numbar makusancinta wanda ya kasance kawunta aka kira shi. Bayan an saka mata allura ana yi mata karin ruwa ne kowa ya fita sai likita da Yusra. Suna jin shiru Rumana ta bude idanu tare da saukowa daga kan gadon ta durkusa a gaban likitan "doctor ka taimakeni idan Uncle dina yazo ka fada masa ulcer ta kusa cinye hanjina" Duk da ya dauki maganar rainin wayo amma bai san lokacin da dariya ta subuce masa ba. Sai kuma yayi saurin daure fuska. "Nayi miki kama da abokin wasanki ne ko me?" Yusra ma durkusawar tayi "idan baka taimaketa ba wallahi yunwa zata kasheta a gidansu. Ulcer din gaske ce zata kamata" Juyawa yayi zai fita Rumana wadda ta tabbatar idan hakkansu bai cimma ruwa ba yau kila banda yunwa jikinta sai ya gayamata a gida bata san lokacin da ta fizge hannu daga jikin allurar ta ruga ta tare kofar ba "idan baka taimaka min ba wallahi zanyi muku hauka a asibitin nan. Ka fada masa mugun ciwo ya kamani a kaini gidanmu kada na mutu a nan" Saroro yayi yana kallonta. Bai ankara ba ya ga ta nufi gadon dakin ta daga shi da yake ba wani nauyi ne dashi ba ta kifar. Dan tebur din kusa da gadon ma hantsila shi tayi tana ihu da kuka. Yusra wadda tare sukayi shirin ciwon karyar ma sai da ta tsorata ganin da gaske Rumana tana neman yin hauka. Suna haka likitan yana kokarin riketa taji muryar kawunta daga dan karamin reception din yana tambayar inda take. Idanunta cike da hawaye ta sake kallon likitan alamun roko da neman agaji. Tausayi ta bashi, ita kuwa Yusra kuka take yi. Awaisu yana shigowa dakin ya ganta biji-biji kamar anyi wasan kura da ita. Ga hawaye ya wanke mata fuska. Da saurinsa ya karasa inda take ya rikota "Rumana me ya same ki? dena kukan ki fada min abin da kike so" Kasa magana tayi sai kukan da ta cigaba da yi. Ba a son ranta tayi wannan abin ba amma idan ba gaban iyayenta ta koma ba bata jin zata iya cigaba da hakurin zaman gidansa. Hankali a tashe ya dubi likitan "me ya sameta?" Hadiyar yawu yayi yana kallon yadda 'yan matan suka tsare shi da idanu "uhmm a binciken da nayi yarinyar nan tana fama da ulcer sosai har tana neman lahanta mata hanji" mamakin kansa yayi da biye musu harda aron kalamansu. Girgiza kai yake yi alamun rashin yarda "Ulcer, ulcer ciwon yunwa? Mtsew, ba dai a gidana ba wallahi." "Abin da bincike ya nuna kenan ranka ya dade" Tuni likita ya fara tsorata kada a daga maganar gaba. Harzuka yayi "kasan ko ni waye zaka kira min ciwon yunwa? To ko maigadin gidana bazai kira yunwa ba balle 'yata" Gaban likita ya fadi a zuciyarsa yace 'yarsa kuma, wace 'ya ce zata yiwa iyayenta sharri irin wannan. Harara ya jefa musu duk da ba kallonsa suke yi ba. Awaisu ya katse masa tunani " kaga ka sallameta zan kaita babban asibiti." Bai jira amsarsa ba ya ya durkusa ya dauko takalmanta ya saka mata sannan ya kamata suka fita. Wani irin tausayinsa ya kamata. Sai dai ko ana muzuru ana shaho da yardar Allah sai ta koma garinsu. Suna shiga mota taji ya umarci dreba da ya kaisu asibitin kudi da iyalan gidansa suke zuwa. To kada karyarta ta kare kawai sai ta sandare masa tana mimmikewa. Hankalinsa ya kara tashi. "Uncle babu inda zani, ka mayar dani gida na mutu gaban Mama. Kada na mutu ban sake ganinsu ba" A take ta karyar masa da zuciya. Asibitin dai yasa suka karasa sai dai a binciken gaskiya an tabbatar masa da gaske bata da kuzari. Tana bukatar hutu da abinci mai gina jiki. Wannan jawabi ya sanya shi cikin rudani. Duk yadda yaso su kwantar da ita fafur taki yarda ita Mama kawai take son gani. Gida suka koma yayi ta fadan yaya akayi bata cin abinci ba'a sanar dashi ba. Maamu mahaifiyarsa ita tayi jinyar Rumana a ranar. Da gaske ta rinka sambatu tana kiran babarta ko runtsawa basuyi ba. Dole washegari yayi shiri shi da dreba zai mayar da Rumana gida. Sai dai yana tunanin me zai fadawa dan uwansa a matsayin dalilin da yasa ya dawo da ita. Suna fita Maamu ta leko ta tagar dakinta tana kallonsu. Hawaye taji ya taho mata mai zafi tana tunanin yadda karamar yarinya ta samarwa kanta mafita. Ita kuma ta yaya zata ta bar gidan dan da ta haifa a cikinta? [19:52, 1/25/2018] 鈥�+234 806 812 5769鈥�: *KASHE FITILA*馃挕2 *Batul Mamman*馃挅 *Fika LG-Yobe State* Yara ne suke ta tsalle-tsalle a tsakar gida saboda yau alhamis babu makarantar Islamiyya. Masu dan girman kuma musamman matan kowacce ta kama aikin gida tana yi. Sallamar da suka ji ce tasa suka tashi babu babba babu yaro suka tafi tarbo mai yinta. Murnar ganin Kawunsu suke yi sai dai ganinsa rike da Rumana tana tangadin karya yasa suka yi cirko cirko. Sarkin surutun gidan ne ya ruga ciki yana sanarwa ga Rumana ta dawo. Mahaifiyarta wadda ta kasance mata ta biyu cikin matan gidan bata san lokacin da ta janyo hijabi ta fito ba. Addu'a take yi Allah Yasa ba wani abin Rumanan tayi ba Kawunta ya kasa zama da ita. Ko da ta fito sauran matan gidan wato uwargidan da amaryar duk sun fito suna musu maraba. Ganin yanayin Rumana yasa suka san babu lafiya. Maman Antu kamar yadda ake kiran uwargidan ita tayi saurin riko hannunta suka shiga babban dakin da yake mazaunin falo a gidan. Tuni Awaisu ya wadata musu shi da kayan kallo da kujeru masu kyau. Bai bi bayansu ba ya wuce dakin Baaba Hure. A zaune ya sameta tana jiran shigowarsa tun bayan taji an ambaci sunansa da na Rumana. Sai da ya gaisheta cikin yarensu na Bolewan Fika sannan yayi mata bayanin dalilin zuwansu. "Kuma ka tabbata ba aljanu bane da ita?" "Ko daya Baaba, jiyan nan dai ta bani tsoro shiyasa nace bari na kawota ta huta kwana biyu. Makarantar tasu zanje sati mai zuwa duk da sun san bata da lafiya na sanar musu halin da ake ciki" "To Allah Ya sauwake, ina 'yar uwata? Kwana biyu ko a waya idan nace yayanka ya kira ba ma samunta" Dan murmushi yayi "tana nan lafiya, kinsan sai ta ajiye wayar ta manta inda take ma. Alhaji bai dawo bane?" Kafin ta bashi amsa suka jiyo muryar Alhaji Harisu yayansa. Dakin ya karaso suka gaisa inda ya sake labarta musu dalilin zuwansu. Wannan karon harda matan gidan da Rumana a wurin. "Zancen banza" cewar Alh Harisu "Shine zaka biye mata ka baro aikinka ku taho" Rumana ta tsuke baki, fatanta kada Alhaji ya bata shirin da suka kwashe sati uku suna yi ita da Yusra yace ta koma wannan kurkukun. Ita yanzu ko sunan Abuja ma bata son sake ji. Shi dai Awaisu lallabata yace ayi kuma a tambayeta dalilin kin cin abinci. Domin ko mutan gidan suna ganinta sunyi korafin ramarta. Yarinyar da ko da tana makarantar kwana kafin komawarta Abuja da kibarta. Ita ko ramar nan ta kewar gida bata yi. ***** Washegari da sassafe Awaisu da drebansa suka kama hanya. Sai da Rumana taji tashin motarsu tayi wata kyakkyawar ajiyar zuciya. Za taci karenta babu babbaka, ta mike kafa taji dadin rayuwarta. Abinci kuwa tun daren jiya take yi masa cin hauka. Bayan kwana biyu da dawowarta suna daki ita da babbar yayarsu da tazo daga gidanta. Hira suke yi Rumana tana bata labarin horon da akeyi musu a gidan Kawun nasu. Karshe ma tashi tayi tana kwatanta irin abin da tayi a clinic din makaranta. Mahaifinsu ne yazo ya tsaya yana sauraren bayaninta batare da ta sani ba. Ita kuma Maryama yayarta da ta ganshi ta kasa cewa tayi shiru sai kai da ta sunkuyar. Tana cikin nuna mata sandarewar da tayi a mota ta kula da Alhajin. Nan jiki ya fara rawa, kanta yayi yana duka ko ta ina. "Har kinyi wayon yiwa dan uwana sharri Rumana?" Ihu take yi tana kuka "Wallahi Baba ba karya nake ba. Ba'a bamu abinci sosai a gidan. Daga ni har Maamu bama koshi" "Rufe min baki sakarai mara godiyar Allah. Sharrin naki harda Maamu a ciki? To zan kira Awaisun da kaina muyi magana" A fusace ya fita ya shige dakinsa. Ko zama baiyi ba aka sanar dashi Baaba tana kiransa. Ya tashi ya fita. "Ina gidan nan kake hukunci irin haka ko? duk kiran da nayi maka kuma baisa ka dena ba" "Kiyi hakuri Baaba wallahi banji ba" Abubuwan da Rumana ta fada ya maimaita mata. Gyada kai ta rinka yi har ya gama. "Babu abin da ya dace kayi da ta fadi maganar nan sai bincike ba duka ba." Cike da mamakin rashin gaskata zancenta yace "bincike kuma Baaba? Awaisu fa ake magana" "Na sani, fada maka ne kawai banyi ba amma dan zaman da nayi kwanakin baya banji dadi ba. Kuma kasan Maamu da zurfin ciki" Kallon mahaifiyarsa yayi yana mamakin maganganunta. Fita yayi yasa aka kira masa Rumana. Ya tsareta da jan ido yace ta fada masa komai tsakani da Allah. Kamar an kunna rediyo haka ta rinka bashi labari kuwa. Tana yi tana kuka, shi kansa Alh Harisu idanunsa kamar gauta don bakinciki da bacin rai. Sallamarta yayi da gargadin kada kowa yaji maganar nan sai ya gama bincike. Wayar kaninsa ya kira suka gaisa tare da taba barkwanci sannan yace ya hada shi da Maamu. Anyi sa'a yana gida da kansa ya kai mata wayar. A zaune take sanyin AC yana neman illata ta amma ta kasa kashewa saboda karamin dansa Safwan ya kwashe batiran remote din ya saka a game dinsa. Da ya shiga hankalinsa bai kai kan rawar darin da takeyi ba balle ya taimaka mata. Wayar kawai ya mika mata. Tana karawa taji muryar Harisu sai kwalla wadda tayi saurin mayarwa. Rabon da suyi magana wane wata biyu. Gaisheta yayi ta amsa muryarta tana rawa. Hakan da yaji kawai ya fahimci tana cikin matsala. Bai zurfafa tambayoyi ba yaje ya sanar da Baaba gobe zaije Abuja taho da Maamu. Ganin ransa a bace sosai yasa ta dakatar dashi yana kokarin fita "kada ka manta Awaisu danta ne na cikinta, bata nemi taimako ba kada kayi shisshigi. Garin neman kyautata mata ka shiga hurumin da baza'ayi maraba da kai ba" Cak ya tsaya yana auna maganar Baaba Hure. "Yanzu sai kawai mu zuba ido idan har gaske ne tana cikin matsala a gidan?" "Ba ido kawai zamu zuba ba kuma bazamu yi gaggawa ba. Komai na duniya a sannu ake binsa har a gano bakin zaren. Misali yanzu Rumana karya tayi mana, da wane ido zaka kalli kaninka ko Maamu idan suka ji?" *Labarin Maamu* [19:52, 1/25/2018] 鈥�+234 806 812 5769鈥�: *KASHE FITILA*馃挕 3 *Batul Mamman*馃挅 *Tuna baya* Da alamun gajiya ya shigo gidan yana daga kafa da kyar. Baaba ce ta fara ganinsa ta taso da sauri. "Yaya Awaisu an dace?" Girgiza mata kai yayi a hankali zuciyarsa a cunkushe da bakinciki. "To kada ka damu, rabon mutum komai nisan lokaci zai zo gareshi. Ka wuce dakina abincinka yana can" Cikin sanyin jiki ya wuce ta bishi da kallo. Sai da ta ga fitowarsa da kwanon abincin ta mayar da hankalinta ga Maamu da take zaune tsakiyar matan Harisu guda biyu tana tayasu tsinkar zogale. Dan daure fuska tayi cikin wasa tace "Kina kallon dana ya dawo ko sannu balle ki tambayeshi yadda akayi?" Maamu murmushi tayi "tunda kina kusa meye nawa a ciki. Da dai bakya nan sai nayi muku kara" Baaba ta hau mita ita Maamu bata kyauta mata ba. Matan Harisu suka sa dariyar rigimar surukansu. Da suka gama Maamu ta tashi ta shige dakinta ta dan turo kofar. Hawaye ne ya taho mata ta sanya habar zaninta ta goge. Tun dawowar Awaisu tana ganin yanayinsa zuciyarta ta karye. Daurewa kawai ta rinka yi tana yaken dole. Shekara biyu kenan yana neman aiki har yanzu shiru. Ita kam Allah Ya sani ta kure matakin jin kunyar Baaba Hure da Harisu. Wanda ya kawota gidan ya jima da rasuwa gashi nauyinsu ya dawo wuyan dansa. Lokacin da ta auri Mal Sa'adu Abali da danta na auren fari Awaisu tazo. Shekararsa biyu mahaifinsa ya rasu. Yana da shekara hudu ta hadu da Malam har sukayi aure. Taso mayar da shi wurin dangin mahaifinsa amma sam Malam yaki yarda yace bai ga amfanin auren mace kuma a kyamaci 'ya'yanta na wani gida ba. Zaman lafiya suka yi sosai da Baaba Hure. Ita Baaba mutuniyar Katsina ce. Cirani ya kawo iyayenta garin shiyasa ta tashi da iya yarensu. Amma duk da haka tana Hausa da 'yan uwanta. Malam da Maamu wadda ainihin sunanta Safara'u duk 'yan Fika ne, yaren Bolanci sukeyi. Kuma haka duka gidan har yara da shi suke tashi sai dai suna Hausa kadan kadan saboda cudanya da Hausawan cikin gari. Baaba Hure yaranta hudu. Baraka, Harisu, Ummukulsum da autarsu Zakiyya. Mace ce mai kyaun hali da sanin ya kamata. Sannan mai jajircewa wurin tarbiyar yara. Domin yaran sunfi tsoronta akan Maamu mai sanyi. Ita dai barta da yawan murmushi ko da ranta ya baci. Haka suke zamansu gwanin sha'awa. Malam ya sanya Awaisu a makaranta Harisu ne yake rakashi domin autarsu ma ta girmi Awaisu da shekara shida. Yana aji biyu a sakandire Malam Sa'adu ya rasu. Maamu ta shiga tashin hankali saboda bata haihu ba a gidan tana gudun su bukaci ta tashi bayan an raba gado. Sanin cewa yanzu gidansu ko ta koma babu inda zata zauna saboda yayyenta duk sunyi aure da matansu a cikin gidan iyayensu yasa Baaba Hure tace ta cigaba da zama dasu tamkar gidanta. Karatun Awaisu kuma 'yar buga bugar da Harisu yake yi da nata jarin suka hada suna biya masa kudin makaranta. A haka ya kammala ya fara shirin jami'a. Maamu ta sayar da gonarta ta biya masa kudin ya tafi Abubakar Tafawa Balewa University (ATBU) ta Bauchi inda ya karanci Banking and Finance. Lokacin nauyi ya fara yiwa Harisu yawa ya soma tara yara. A haka dai da karume karume suka rinka tallafawa har ya gama da sakamako mai kyau. Ga shakuwa tsakanin 'ya'yan gidan wanda bai sani ba bazai taba gane cewa Awaisu ba dan Malam bane. A halin yanzu aiki yake nema ruwa a jallo abu ya gagara. Maamu kullum burinta ya sami abinda suma zasu gwadawa Baaba Hure da zuri'arta karamci ba don su biyasu ba. Sai don kawai ta nuna musu cewa bata taba manta alkhairinsu ba gareta. Harisu ya kara aure iyali suna ta karuwa. Ya ciyar da dolensa ya ciyar da ita da danta. Wannan yasa take jin babu dadi. ***** Bayan kwana biyu Harisu yaje Kano saro kaya a Kantin kwari kamar yadda ya saba duk karshen wata. Sunansa yaji an ambata ya juya yana neman mai kiran. Murmushi ya saki tare da sassarfa wurin karasawa wurin wani mai shago suna dariya tare da rungume juna "Harisu Abali" "Saminun Kano" Sake rungume juna sukayi sannan Saminu ya ja hannunsa suka shiga cikin shagon atamfofi. Lemo mai sanyi yasa aka kawo masa sannan ya bayar da kudi a siyo musu abinci. "Ikon Allah, ashe rai kan ga rai" cewar Saminu yana kara kallon abokinsa. "Ga zahiri dai, sama da shekara biyar sai yau Allah Yayi ikonsa" Hira sukayi sosai ta yaushe gamo. Saminu yayi zaman Fika inda suka saba sosai da Harisu. Daga baya ya dawo garinsu Kano ya cigaba da kasuwancinsa. A hirar yake tambayarsa kaninsa ya fada masa ai har ya gama jami'a. "Aiki fa?" "Nan fa daya, yanzu ma tare muka zo zai fara tayani kasuwanci kawai kafin aikin ya samu. Yanzu ma yana Wambai wurin masu robobi" Harisu da Saminu sun sha hira sannan suka yi sallama da alkawarin haduwa washegari kafin su koma Fika. **** Washegari kafin azahar sun isa shagon Saminu yi masa sallama. Yana ta tsokanar Awaisu an girma an dena kiran Yaya da an taba shi. Ya hada musu 'yar tsaraba daidai misali sannan ya ja Harisu gefe. "Mutumina nayi maka karambani fa, jiya bayan rabuwarmu naje gidan wani tsohon dan kwangila da nake sayar wa shadda" "Kana nan da shige shigen ka mutumina" Harisu ya fada yana murmushi. "Me za'a fasa..yanzu dai mu bar wannan zance. Cikin hira nayi masa bayanin ina da kani da ya gama karatu yana neman aiki. Sai dai anyi rashin sa'a bansan me ya karanta ba. Shiyasa bayanin nawa bai cika ba" Farinciki sosai ya bayyana a fuskar Harisu " da gaske kake?" Murmushi yayi ganin abokin nasa yaji dadi "yanzu dai yace sati mai zuwa zashi Abuja wurin wani kusar gwamnati. Shine yace idan zai yiwu Awaisu ya same shi a can ranar alhamis" Kati ya dauko mai dauke da sunan mutumin da nambar wayarsa ya mika masa. "Gashi Allah Yasa a dace. Idan yaje sai ya fada masa cewa shine kanin Saminu Zawachiki" Harisu ya rike hannuwansa ya ma rasa kalmar godiya "idan munje zaka ce. Ai dole na rakashi. Allah Ya baka ladan zumunci." Yafito Awaisu yayi da hannu ya matso kusa dasu ya fada masa halaccin da Saminu yayi musu. Shima godiyar yake yi kamar zasu ari baki su biyun. [19:52, 1/25/2018] 鈥�+234 806 812 5769鈥�: *KASHE FITILA*馃挕4 *Batul Mamman*馃挅 Ranar laraba da yamma Harisu da kaninsa suka isa Abuja. Da tambaya suka karasa gidan Alh Mudi Maibuta, dan kwangilan da Saminu ya nemi taimakonsa akan neman aikin Awaisu. Gida ne babba irin na mutanen da naira ta zauna musu. Daga bakin gate din maigadi ya tambayi sunansu da abin da ya kawosu. Suna fada ya saki fuska tare da sanar dasu Alhaji ya bayar da umarnin yi musu iso da zarar sun karaso. Wurin wata katuwar bishiya ya rakasu inda Alhajin yake zaune yana shan iska. Gefensa 'yan mata ne guda biyu sanye da kaya iri daya. Tun tahowarsu Awaisu wurin babbar ciki ta kafe shi da ido tana murmushi. Shi kuwa hankalinsa bai ma kai gareta ba. Cike da girmamawa suka gaishe da Alh Mudi. Shima fuska a sake ya amsa musu sannan yace su shiga wani daki kusa da na maigadinsa. Abinci yasa aka kawo musu aka yi musu tarba a mutumce. Sai da suka ci suka koshi sannan ya dawo ya karbi takardun Awaisu. Murmushin fuskarsa ya fadada "Ikon Allah ashe kaima Bauchi kayi karatu. Kila ma ka taba haduwa da Gimbi." A ladabce Awaisu yace "Wane ne hakan?" Alh Mudi ya hau dariya "Yarinyar wajena ce, sune a zaune ita da kanwarta shigowarku dazu. Da yake sunan mahaifiyata gareta shine nake kiranta Gimbiya. To kuma kasan mutane, a hankali sunan ya koma Gimbi." Harisu da Awaisu suka gyada kai suna Allah Sarki. Alh Mudi ya cigaba da bayaninsa "Shekararnan ta gama ATBU din amma Business admin ta karanta. Nayi magana da wani sun karbeta a banki zatayi bautar kasa. Shine kaga ina dariya da na ga kaima bangarenka kenan, to zan tura masa takardunka gobe. Kaga abin ma duk zaizo da sauki" Godiya da addu'a suka rinka yi masa. Murmushi kawai yayi "Saminu akwai kirki. Kaya kawai nake saya a wurinsa amma ina jinsa kamar dan uwa saboda iya mu'amalarsa da mutane" Harisu yace hakane domin shima shaida ne. Daga nan Alh Mudi ya yace lallai sai Awaisu ya zauna a Abujan domin idan ya bayar da takardun washegari mai yiwuwa zuwa litinin a bukaci ganinsa a bankin. Sannan yayi alqawarin bashi makwanci har zuwa lokacin. Harisu ya rasa bakin godiya. Mutanen kirki basa karewa a duniya. Sai dai haduwa dasu dace ne. Duk kudin Alh Mudi Maibuta bashi da dagawa da girman kai. Da safe Harisu ya koma Fika bayan yaja kunnen dan uwansa akan ya kula da kansa kuma ya kame mutumcinsa. ***** Tun tafiyar yayansa baya fita ko'ina. Kullum yana daki sai sallah da take fitar dashi wadda Alhajin ko wani saurayi da Awaisu bai tantance matsayinsa a gidan ba suke jagoranta. Safe, rana da dare maigadi zai miko masa abinci ya karba da godiya. Yau lahadi sun idar da sallar magariba Alh Mudi yace ya shigo falonsa su gaisa da iyalin gidan. Domin idan har ya sami aiki an barshi a nan Abujan to dole kafin ya sami wurin zama nan zai cigaba da zama tare dasu. "Ni kuma ba mazauni bane, shiyasa na ga ya kamata kasan mutanen gidan suma su san ka" A baya ya bishi suka shiga wani falo wanda aka kawata da duk wani abu na jindadi. Kafin su zauna wata mace ta shigo sanye da hijabi da alamun sallah ta idar. Sai 'yan matan ranar da suka zo biyu da wani yaro da suke sallah tare wanda bai wuce shekara goma ba. Awaisu ya gaisheta ta amsa da fara'arta ta tambayi sunansa. Kafin ya amsa babbar wadda yake tsammanin ita Alh Mudi ya kira da Gimbi tace "A.S Abali, Mama shine yayi vice president na S.U.G a makarantarmu" Da mamaki ya dago yana kallonta. Shi dai bazai iya tuna fuskarta ba amma dai abin da ta fada gaskiya ne. Kyaunta kuwa tuni yayi tasiri a zuciyarsa. Maman tace "Gimbi rawar kai, ai ba ke na tambaya ba. Naga yayi shiru ne shine nake son jan shi da hira ya sake damu." Ta koma tana kallonsa "Alhaji yayi min bayanin komai game da kai. Allah Ya bamu ikon zaman gaskiya da amana" "Amin Hajiya nagode. Allah Ya kara girma" "Amin, sai dai Mama ake kirana ba Hajiya ba" Daga nan sun dan taba hira wadda hankalinsa gabadaya yana kan Gimbi. Tunda ta fadi sunansa dazu zuciyarsa take kawo masa sabon tunani game da ita. Sai dai a wurin ya yakice shi. Ai ido ba mudu ba amma yasan kima. Ina shi ina 'yar babban gida irin wannan. ***** Washegari da sassafe ya tashi ya shirya kamar yadda Alh Mudi ya umarce shi. Yana wurin maigadi suka fito tare da Gimbi. Taci kwalliya tayi kyau sosai. A bayan mota ta zauna kusa da babanta shi kuma Awaisu yana gefen dreba. Babu inda ya gane a wurin da suke tafiya sai dai kawai yaga an rubuta Zenith Bank. A reception Alh Mudi ya barsu shi da Gimbi ya wuce wurin manaja. Hira suke tabawa jefi jefi saboda shi dai ya kasa sakewa da ita duk kuwa da cewar ya fahimci sakon da yake boyewa a zuciyarsa itama shine a cikin ta ta zuciyar. Ba jimawa Alh Mudi ya fito ya bukaci Awaisu ya shiga wurin Manaja. Shi kuma suka shiga wani dakin daban da Gimbi. A nan ne aka yi mata bayanin aikin da zata rinka yi. Shi kuma Awaisu takardu ne aka bashi yayi ta cike cike. Bayan ya gama aka sanar dashi zai dawo washegari interview sannan yaje Lagos sati na sama training na wata daya daga nan ya jira posting. [19:53, 1/25/2018] 鈥�+234 806 812 5769鈥�: *KASHE FITILA*馃挕5 *Batul Mamman*馃挅 Abu kamar wasa sai gashi komai ya kankama dangane da samun aikinsa. Awaisu ya koma Fika sanar da mutan gidan halin da ake ciki da tafiyar da zaiyi Lagos. Kafin ranar tafiyar Maamu ta tura shi wurin yayanta ya karbo rago biyu cikin tumakin da ake yi mata kiwo ya sayar. Da kudin wanda ko sisi bata cire a ciki ba tace yayi kudin mota da guzuri. Kamar kullum kyakkyawar addua yayi mata tare da godiya. "Ba godiya zakayi min ba. So nake idan kaje ka dage yayi abinda ya kaika. Lokaci yayi da ya kamata ace kana da iyali kaima sannan ka fara ragewa dan uwanka nauyi. Ga zuri'a Allah Ya bashi sosai. Kaga yanzu cikin yaran sai ka rinka biyawa wasu kudin makaranta idan ka fara daukan albashi" "Maamu kenan, Allah Ya bani iko. Nifa babban dana ma sunansa Haris. Tun yanzu ya kamata ki fara kirana Abu Harith irin na Larabawa" Neman abin da zata buga masa tayi saboda rashin kunyar da yake yi a gabanta. Ba shiri ya tashi ya gudu. Bayan kwana biyu Harisu ya raka shi tasha ya wuce Lagos. Watansa daya wurin induction din sababbin ma'aikatan banki. Ana gamawa ya koma Abuja domin jiran posting. A wannan lokacin ne kuma soyayya mai karfi ta shiga tsakaninsa da Gimbi. Tun yana ja da baya har ya amince. Ji yake yafi kowa sa'a. Mace kamarta tana soyayya da talaka irinsa. Da taimakon Alh Mudi ya samu aka barshi a Abuja maimakon Ilorin da aka tura shi da farko. Ganin yana da kwanaki goma kafin lokacin fara aikin ya hada kayansa sai gida. Gimbi harda kuka da zai tafi saboda sonsa take da gaske. Alkawari yayi mata cewa bazai wuce sati ba zai dawo sannan suka rabu. Yana isa gida yara suka fito ana ta murnar dawowarsa. Ya shiga ciki nan ma su Baaba sai murna aiki ya samu. Nan yake jin kwanaki hudu da suka wuce matar Harisu ta biyun ta haihu. Kai kace shi aka yiwa haihuwar ya fita neman dan uwanansa yana murna. ***** Washegari suna zaune a bakin shagon Harisu suna hira Awaisu yace ya zabawa jaririya suna Ummu Ruman. Amma Rumana za'a kirata. "Kai kuma a ina kaji wannan sunan" Harisu ya tambaya yana kallonsa. "A littafin tarihi" "Idan munje gida sai kayi mata huduba dashi" cewar Harisu Duk da cewa ya riga yayi mata da suna Aisha amma baya son batawa kaninsa. Shima kuma Awaisun da yasan da hakan bazai taba kawo wani sunan ba. Sai yamma suka koma gida. A bakin kofa ya tarar da dansa na biyu yana shirin fitowa. "Sarkin yawo ina zaka da yamman nan" "Baba kayi bako daga Kano. Shine aka ce na kirawo ka" Harisu ya shiga ciki dakin Baaba inda suke yana tunanin waye yazo. Abin mamaki Saminu ya gani tare da matarsa da yaransu biyar. Tsabar murna ya rungumeshi suna dariya. "Bala dreban tifa ne ya fada min haihuwar nace to lokacin tada zumuncin mu fa yayi. Dole mu hada kan iyalinmu." "Sosai kuwa, sannu yaya hanya" Matar Saminu mai suna Amina da yaransa duk suka gaishe da Harisu. Ana ta barkwancin yadda zasu rinka magana tunda Hausa a gidan bata zauna sosai ba. Baaba da Awaisu sune masu Hausar sosai. Awaisun shima ya shigo suka gaisa. Fita yayi sauran kudin hannunsa yasa ya siyo lemo, kaji da kwai ya bawa Maman Antu uwargidan Harisu domin karrama baki. Yaushe zai manta Saminu a rayuwarsa. **** Kwanansu hudu a gidan duk an saba kamar sun dade tare. Yaranma kowa da abokin sa ban da babbar wadda ta girmi duka yaran gidan. Ana gobe zasu tafi ne Harisu da Saminu sun zauna hira da daddare Harisu ya sako zancen da yake ta son yi. "Mardiya shekararta nawa ne yanzu?" "Ka ganta tayi tsayi ko? Shabakwai zatayi da azumi. Badi zata gama sakandire in sha Allah" Harisu yayi murmushi "To Allah Yasa abin da zan zo dashi yayi maka. Nace mai zai hana mu hadata da Awaisu?" Saminu ya kalle shi sosai "da gaske kake yi?" "Indai ka amince. Wallahi Saminu ban taba ganin mutum irinka ba. Halayenka abin koyi ne ga wasu. Idan na bari damar nan ta wucemu ai na cuci zuri'ar Awaisu. Mai alkhairi irinka dole a kyautatawa 'ya'yanka zato" Saminu ya kama hannunsa kam "in dai haka ne na bawa Awaisu Mardiya halak malak inyi maka ta yara" Dadi ya kama Harisu suna dariya "in sha Allah Awaisu bazai bamu kunya ba. Dama watan da ya wuce na gama biyan su Zakiyya kudin gidan Malam da ya fada rabonsu a gado. Gyara shi zanyi sosai kafin shekara mai zuwa shima Awaisun ya tara abin da ya tara sai su zauna a ciki. Ba munyi maganar a Abuja zaiyi aiki ba? To muna sa rai zai sami muhalli kwanan nan. Kaga sai su koma can ya sa ta cigaba da karatu ma" Saminu farinciki ya cika zuciyarsa. Shi yana yiwa Harisu kallon mutumin kirki. Shima Harisun kallon da yake yi masa kenan. Sun yanke shawarar sanar da Mardiya babbar 'yar Saminu da Awaisu shawarar da suka yanke domin jin ta bakinsu da kuma basu hakkinsu don kada a zalinci kowa. Awaisu wanda yake bayan kofa tun bayan yaji an ambaci sunansa ya fasa karasawa wurinsu. Ji yayi kamar an dora mada dutse a kansa. Shi kadai ya soma magana a hankali "yanzu wannan yarinyar da bata gama zama mace ba za'a bani? Wallahi da sake. Ko ban hadu da Gimbi ba babu inda zan kai wannan yarinyar" [19:55, 1/25/2018] 鈥�+234 806 812 5769鈥�: *KASHE FITILA*馃挕6 *Batul Mamman*馃挅 Tun daga wannan rana Awaisu yake wasan buya da Harisu. Duk inda yasan zasu hadu su kebe guduwa yake yi. Ranar da zai koma Abuja ma kamar ana korarsa don sauri. Haka ya tafi tasha kafin Harisu ya dawo daga shagonsa inda ya ajiye masa kayan amfani kamar su madara da ganyen shayi da yake son bashi guzurin tafiya. Baiyi sati da komawa ba Alh Mudi ya dawo daga Kano. Wata rana da yamma ya tura karamin dansa ya kirawo Awaisu. Da ya zo ne ya tabbatar masa da Gimbi ta sanar dasu abin da ke tsakaninsu. Karshe yace yana so ya sanar da yayansa cewa su same shi a Kano shi da Saminu idan har da gaske yana sonta da aure suyi magana. "Ban yarda da bata lokaci ana soyayya ba indai akwai halin yin auren gara ayi kowa ya huta." Gaban Awaisu ya fadi jin Alh Mudi ya ambaci ganin yayansa da Saminu. To da wane idon zai kallesu ma. Shi dai Alh Mudi bai san me yake faruwa ba. Albarkacin Saminu yake ganin lallai Awaisu ma mutumin kirki ne kamar yadda ya kula a dan zaman da yayi dasu. Bai sami damar komawa gida ba sai bayan sati biyar ana hutun Good Friday da Easter Monday. Haka ya tafi jiki babu kwari saboda rashin sanin yadda zai tunkari dan uwansa da maganar auren Gimbi. Gashi Alh Mudi yace su same shi a gidansa na Kano. A son ransa ayi bikin bayan sallah karama tare da na babban dansa wanda suke a Kanon tare da babarsu uwargidan Alhaji. ***** Kwanansa biyu da dawowa ya rasa abin da ke masa dadi kuma ya kasa fadawa kowa. Maamu tayi fadan da magiya duka yaki cewa komai. Gashi yana matukar son Gimbi baya fatan rasata. Da daddare yana kwance a dakinsa Harisu ya shigo. Ya tashi zaune amma ya kasa cewa komai. Harisu yayi murmushi yana kallonsa. Sai da ya zauna a gefen katifar dakin ya soma magana. "Yanzu ni kake gudu saboda ka soma aiki a Abuja kayi kudi ko. Kana ganin kafi karfinmu." Awaisu ya zaro ido a razane "Yaya me ya kawo wannan zancen kuma? Wallahi ba haka bane. Allah Ya kiyaye. Bana fatan abin da zai kawo min tunani makamancin haka" Harisu ya daure fuska "haka kawai za ka fara guduna ne idan ba kana tsoron a ganka tare da talaka irina ba." Idanun Awaisu tuni suka yi ja saboda rashin jindadin kalaman yayansa. Shi da ya dauki Harisu uba yaushe ma irin wannan tunanin zai zo masa. "Wata matsalar ce daban Yaya" Ya fada a raunane. Harisu yayi dariya a zuci domin ya samu Awaisu ya fada tarkon da yayi masa na son jin damuwarsa. "Ina jinka, menene matsalar da take hanaka walwala a gidan nan?" Babu amfani cigaba da boyewar shiyasa ya fada masa maganar da yaji sunyi da Saminu da kuma wadda suka yi da Alh Mudi. Wani dogon numfashi Harisu ya ja. Ya jima yana tunani kafin ya soma magana cikin nutsuwa. "Kai ba yaro bane da zan ce baka san abin da kake yi ba. Sannan ka wuce ayi maka auren dole. Duk yadda nake son ka auri Mardiya ba ni zan zauna maka da ita ba. Saboda haka nagode da ka fada min da wuri kafin ayi auren muji kunya. Zanyi kokarin fahimtar da Saminu. Kuskurena ne da ban fara maganar da kai ba na fada masa" Ko bai fada ba yasan ransa a bace yake kawai ya danne ne "Kayi hakuri Yaya. Itama Gimbi tana da kyawawan halaye idan ka ganta ....." Bai karasa ba Harisu ya mike batare da yace komai ba yayi hanyar fita. Tunaninsa bai wuce yadda zai fita kunyar Saminu ba. Tsayawa yayi ba tare da ya juyo ba yace "ka shirya muje Kanon gobe kafin lokacin komawarka aiki." ***** "Zancen banza kai, ina Awaisu ina 'yar masu kudi. Ko kuwa so yake ya janyo ace yayi auren jari? To ma a ina yake tunanin ajiyeta idan anyi auren. Yaushe ma ya fara aikin da zai jajibo aure irin wannan" Maamu ce take ta fada bayan Harisu ya sanar da ita da Baaba batun tafiyarsu Kano neman aure. Haka tayi ta fada yana bata hakuri da nuna mata magana kawai zasu je yi ba auren za'a daura ba. Ranar da suka isa Kano Saminu jiki a sanyaye ya tarbesu. Wannan ya dagawa Harisu hankali ko har Alh Mudi ya sanar dashi komai. Baya son abin da zai taba alakarsu ko kadan. Shi Awaisu dama ya kasa kallonsa ma. Tunda suka zo yake sunkuyar da kai. Bayan sun dan huta ne suka zauna tattaunawa. A nan Saminu ya dubi Harisu "Alh Mudi yazo gidan nan da kansa akan yana son na bawa dansa auren Mardiya. Sanin cewa munyi magana da kai nace na bayar da ita ga Awaisu. Shine yayi min wani bayanin daban da ban gama fahimta ba " A kunyace Harisu ya fada masa abin da ke faruwa. "Kayi hakuri abokina, bani da masaniya akan hakan. Da tun farko bazan bijiro da maganar hadasu ba" Awaisu duk sai yaji babu dadi. Yanzu da Alh Mudi baizo nemawa dansa ba shikenan ya bata zumuncin abokan. Muryar Saminu ce ta katse masa tunani "Babu komai, ai kaga yadda Allah Yake nuna ikonSa. Sai muje gidan ka fada masa ka bada auren Mardiya ga Fawaz a matsayin waliyinta tunda bani da dan uwa namiji. Shi kuma Awaisu sai na nema masa auren Gimbi" Sai a lokacin Harisu yayi murmushi hankalinsa ya kwanta ganin Saminu bai dauki abin da zafi ba. Washegari kuwa suka dunguma sai gidan Alh Mudi aka daidaita magana. Sallah karama da sati biyu aka sha bikin Awaisu da Gimbi. Ganin cewa bai samu muhallin kirki ba Alh Mudi ya bashi gida da sunan Gimbi a Abuja inda zasu fara zama kafin ya sami nasa. Ita kuma Mardiya suka tare a Kaduna ina Fawaz yake aiki. ***** *Bayan shekara 12* Cikin shekarun da suka gabata Awaisu ya sami budi sosai. Domin har gida ya gina kato a Abuja yana shirin tarewa. Inda Allah Ya kara taimakonsa shine kasuwanci da yake yi. Duk da yana aiki ga rashin lokaci haka ya sami yara biyu 'ya'yan kawunan sa da ya budewa shago suke sayarda atamfa da shadda. Abu kamar wasa sai da ya hada shaguna hudu a jere a Wuse market. Ga kwazonsa a wurin aiki yasa ya sami mukamin manaja a bankin. Gidan Harisu kuwa yasha gyara sosai har mota ya saya masa sannan ya kara masa jari. Zamansu gwanin sha'awa. Tsakaninsu da Gimbi babu wata matsala. Dayake itama aikin bankin take yi bata da lokaci na zuwa Fika sosai. Yaransu hudu babban ciki Haris, sai Daula mai sunan babar Gimbi, Amir mai sunan Alh Mudi da kuma auta Sa'ad suna kiransa Mu'allim. ***** A gajiye Awaisu ya shigo bayan isha yaran suna ta murnar dawowarsa daga Fika. Sai da ya gama dasu ya wuce dakinsa. Sauri yake yi idanunsa su gane masa matar da yake jin bazai taba iya hadata da kowa ba saboda irin son da yake yi mata ga kuma albishir a bakinsa. Taci kwalliya tayi kyau sosai tazo ta tarbe shi tana murmushi "Ashe ka shigo maimakon ka kira kafin ku karaso na hada maka ruwan wanka" Ya shafi gefen fuskarta yana murmushi "kada ki damu, zo ki zauna kiji albishir din da nazo miki dashi har biyu. Dayan ina hanya akayi min waya aka fada min" Kaskon turaren wutan da yake gefen gado ta dauke sannan ta dawo ta zauna kusa dashi yana rungume da ita yayi ajiyar zuciya. "Gimbina Allah Ya yarda. Visa dinku ta fito" Ta dago kai da sauri cikin farinciki "wace visa kuma?" "Dama na boye miki ne sai komai ya tabbata. Na biya muku Hajji ke da Yaya Harisu, Baaba da Maamu. Sai Yaya Zakiyya tunda su Anti Baraka da Ummu mazansu sun kaisu. Kinga za ta tayaki kula dasu Baaba. Albishir na biyu kuma kuna dawowa nake so mu tare a Apo. To babban abin jindadin shine dasu Maamu zamu tare" Shiru yaji Gimbi taki dagowa bare tayi magana. Ko da ya dago kanta hawaye take yi sosai. Wani sonta ne yake shigarsa domin yasan kukan farinciki take yi. Rungumeta yayi yana shafa bayanta. "Dama nasan zakiyi murna sosai Gimbina. Shiyasa ban fada miki batun tafiya Hajjin ba sai da na gama. Tunda kinga ni naje har sauu biyu kuma last year munyi umara tare dake. Shiyasa bazan bi ku ba. " ya cigaba da cewa "Kuma fa yadda naso har da Baaba zamu tare. Sai dai lalurar idonta yasa Yaya yaki yarda. Shine na hakura ba don naso ba. Burina ya cika zan dawo da Maamu kusa in kula da ita. Itama taji dadin arzikin da Allah Ya bani. Ta dade tana jin nauyin su Baaba da Yaya Harisu. Duk da naso hadawa da Baaba hakan bai samu ba. Amma zan dauko Rumana. Gimbina da ina da yadda zanyi fa wallahi Yaya Harisu ya dena fita neman kudi. Komai ni zanyi masa" Can kasan makoshi tace "uhmm hakane." Domin ji take yi ya cikata da surutu mara kan gado. Mikewa yayi ya shiga bandaki domin yayi wanka ko zaiji saukin gajiya. Yana shiga Gimbi ta fice ta tafi dakinta ta rufe kofar da mukulli. Gadonta ta hau ta saki kuka cikin tashin hankali. Ko da wasa bata taba kaunar zama da uwarmiji ko dangin miji ba. Can daga nesa dai yayi musu kyauta suna kauye ba sai sun rabesu ba. "Tabdi, akwai matsala. Matar da ko Hausar kirki bata iya ba sai anyi magana tayi ta yankare hakora tana murmushi. Shine don kana jin ka fara kudi zaka dauko min su ka kawosu ko neman izini na bakayi ba. Da sake Awaisu....bana cikin matan da za'a hada da uwarmiji ace mu zauna lafiya gida daya" Dankwalinta tayi jifa dashi ta rasa me yake mata dadi. Ita fa shi kadai take so ba danginsa ba. Duk halaccin da tayi masa ta aureshi talaka ko gidan zama bashi dashi. Shine yanzu arzikin nasa kuma sai sun raba tare da wadda bata nan lokacin da suke nema. Ta hana kanta sukuni tana fita aiki duk domin ta taimaka masa. Ba don kada ace tayi sharri ba ma sai tace gabadaya gidan Harisu wari yake yi mata idan taje Fika. Shiyasa bata son zama idan taje. [19:56, 1/25/2018] 鈥�+234 806 812 5769鈥�: *KASHE FITILA*馃挕7 *Batul Mamman*馃挅 Gani tayi kukan bazai kaita ko ina ba ta yanke shawarar washegari zata kira Mama ta fada mata. Dole ma a dauki mataki don ba bauta tazo yiwa kowa ba. Shirin bacci tayi sannan ta koma dakin nasa. Kwance ta same shi akan abin sallah da gani sallah ya idar bacci ya dauke shi. Tausayinsa kuma taji, ya mayar da kansa tamkar agogo. Bashi da hutu kwatakwata duk domin ya farantawa su Maamu. Tsaki taja a fili tana tunanin yadda zata bullowa lamarin da ya tunkaro ta. "Saboda zan kawo mahaifiyata gidana shine kike tsaki haka Gimbi?" Muguwar faduwar gaba taji. Shi kuwa ya mike tsaye yana kallonta rai a bace. Bakinta yana dan rawa tace "haba my dear, kada kayi min mummunar fahimta mana. Dazu da kanka ka gani ina murna harda kukan..." "Kukan bakinciki ba. Da farko har ga Allah nayi zaton dadi kika ji ganin yadda na damu da yanayin da mahaifiyata take ciki. Bata da wurin da zata kira gidanta. Sai da nayi wanka na biyo bayanki naji kina kuka sosai a dakinki." Rasa bakin magana tayi shi kuwa ya cigaba da magana cikin kunar rai "Duk duniya bayan Maamu babu wanda ya cancanci kyautatawa daga gareni kamar Yaya Harisu. Ban taba boye miki asalina ba. Amma abin mamaki kina nuna bacin ranki akan kyautatawar da zanyiwa wanda suka zama jigon rayuwata. Idan bazaki iya zama dasu ba sai na auri wadda zata iya" Tun da ya fara magana bata tanka shi ba sai yanzu da ya ambaci kishiya. "Kayi kadan kace zaka auro wata ka ajiye a gidan nan. Ko ka manta cewa nawa ne. Suna na ne a jikin takardun gidan" "Dadin abin nima ina da nawa. " Ta turo baki cike da tsiwa. Tsiwar da a da take bashi sha'awa idan tayi "Haka nan zaka kare rayuwarka kana yiwa wani kato bauta. Sai shegen aure da tara iyali. Kai kuma an barka da siyan shinkafa da ragon suna" Shiru yayi har sai da ta gama maganarta tukunna sannan ya tako gabanta fuskarsa babu annuri ko kadan. Ja ta rinka yi da baya yana binta "Yaya Harisun ne kato Gimbi?" Ya fada a hankali amma kana jin muryarsa har wani rawa take yi saboda bacin rai. Duk da a tsorace take amma ta kule da yadda yake zare mata ido akan 'yan uwansa. "Karya nayi ba katon bane? Ko baiyi biyunka ba" Bata karasa magana ba taji ya gwabje mata baki. Nan take jini ya soma zuba saboda fashewar lebenta na kasa. Cikin kuka tace "Awaisu ni ka fasawa baki?" "Idan baki fita daga dakin nan ba sai nayi miki abin da yafi wannan." Murya ta soma dagawa tana kuka "babu inda zani, gidana ne ba naka na. Idan kaji haushi ka fita ka koma naka" Fitar yayi zuciyarsa tana tafasa. Wai akan iyayensa da bashi da tamkarsu shine Gimbi take yi masa abin da bai taba tunanin zata aikata ba. Lallai ba'a shaidar mutum. Yasan halinta na kyankyami da ji da kai. Shiyasa yake mamakin irin son da take masa farkon haduwarsu. Falo yaje ya samu yaransa uku sunyi bacci sai Haris da yake karasa homework. Tashinsu yayi daga su sai kayan baccin jikinsu suka fice. Motarsa ya bude suka shiga suna tambayarsa inda zasu je. Bai basu amsa ba ya rinka dannawa mai gadi horn. Yana budewa ya fita a guje. Karar horn din ce ta fito da Gimbi. Tsoronta kada da gaske ya fita daga gidan. Sai dai abin mamaki ba shi babu yaran. Nan fa hankalinta ya kara tashi. Mai aikinsu Laminde ta shure da kafa tana bacci itama a falon ta tambayeta ina su Daula "Hajiya gasu nan suna hamok. Jiransu nake yi su karasa aje a kwanta." Ta galla mata harara "ina kika gansu. Aikin banza babu abin da kika iya sai bacci" Waje ta fita inda mai gadi ya tabbatar mata da yaran Alhajin ya fita. Haka ta rinka kiran wayarsa yaki dauka. Karshe ma kashewa yayi yana kallon yaransa suna bacci a makeken gadon dakinsa. Gidansa na Apo ya tafi dasu. ****** Da sassafe yaji ana buga gate ya leka ta taga. Maigadinsa ya gani yana ta washe baki ya budewa Gimbi gate ta shigo. Ko rufe kofar motarta batayi ba ta fito ta shiga gidan cikin sauri. A falo ya sameta yace kada ta tasar masa yara. "Wane irin wulakanci ne zaka daukar min yara cikin dare" "A iya sanina lokacin da muka tare a gidan nan ke kadai kika shigo sai akwatunan kayanki. To mene ne na bacin rai don na kwashe yaran da jinin Maamu yake yawo a jikinsu" "Wai duk saboda maganar jiya da bata taka kara ta karya ba kake min wannan cin kashin harda fasa min baki" Ya tabe baki "ina jin baki san girman uwa bane" Neman sulhu take yi domin tun aurensu basu taba samun sabani irin haka ba. Kwantar da murya tayi ta soma magana "Duk laifinka ne, ta yaya zaka shirya kawo Maamu batare da neman izinina ba? Nima fa ina da hakki akan ka. Kuma abu irin wannan sai ka fara shawara dani kaji nawa view din" "Neman izininki? Wai dama haka kike ne ko kuwa sabon salo ne kika fito dashi kawai don baki son dangina. Ba fa tun yau na san kina nuna musu kyama ba. Sharewa kawai nake yi saboda babu wanda ya taba korafi cikinsu." "Kaga ni ba rigima nazo muyi ba. Maganar fahimta nazo da ita. Idan kana so ka ginawa Maamu sabon gida a Fika is up to you. Amma batun mu zauna tare is out of the question. Zama da suruka baya taba haifar da alkhairi" Duk yadda yake son ta a daidai wannan lokacin yayi nadamar aurenta. Rasa bakin magana yayi yace mata kawai ta fita idan ta gama. Ganin wankin hula zai kaita dare ta ja motarta ta tafi gidansu. Tana kuka ta zayyanawa Mama abin da ya hadasu. Mama ta dubeta sosai ta girgiza kai. "Idan kika kure Awaisu ya sakoki zaki gane kudi da gata aikin banza ne idan aka rabaka da iyalinka. Ke da ya kamata ki nuna masa kinfi kowa farinciki shine zaki bata masa rai akan mahaifiyarsa. To yayi miki adalci ma da bai hadoki da takarda ba. Shashashar kawai. Idan ma zugaki akeyi ki sani aljannarki tana karkashin kafar mijinki. Shi kuma tasa tana tare da mahaifiyarsa. Kada ki zama mace mai kashewa mijinta fitilar rayuwarsa Gimbi. Uwa haske ce, uwa rahamace. Da kika shiga matsala ai gaki a gabana." "Mama yanzu goyon bayansa kike yi" "Ki kiyayeni Gimbi. Kuma ki wuce yadda kika bata mishi rai ki bashi hakuri ku sasanta. Idan Alhaji yaji maganar nan ki kuka da kanki. Kinsan halinsa sarai. Bar ganin yana sonki hakan bazai hana ya saba miki ba" Dukar da kai tayi ta gama jin fadan Mama ta tashi ta koma sabon gidan. Amir ne ya fada mata baban nasu yana daki ta shiga da sallama. Kafin ya amsa ta durkusa gwiwoyi a kasa a gabansa tana kuka. Kamar ya basar sai dai Gimbi matsayinta daban a zuciyarsa. Tasowa yayi yazo gabanta. Cikin kuka da nuna nadama ta rinka bashi hakuri da nuna masa ta gane kuskurenta. Kukan da tayi tana ajiyar zuciya yasa dolensa ya hakura tare da yi mata nasiha. Cikin dan kankanin lokaci ta shawo kansa suka daidaita. ***** Zaune suke cikin daki su biyu ta dubi kanwar Mama wadda take binta bayan ta bata labari. "Anti Bebi wannan ita ce matsalar da ta tunkaro ni. Kuma Mama ta bashi goyon baya" "Ki bar komai a hannuna 'yata. Indai ina raye babu wanda ya isa ya takura miki. Tun da dadewa nace kizo muje a mallaka miki shi a tafin hannuki kika ki yarda ke dadi miji. Yau ga irin abin da nake ta hango miki ya faru. Ke ko babu boka babu malam yayi kadan kinji ko. Shi din me? Mijina na uku ma duk taurin kansa sai da ya koma albashinsa ma a hannuna yake balle wani Awaisu." Kalmar karshe ta sosawa Gimbi rai sai dai biyan bukata yafi dogon buri [19:56, 1/25/2018] 鈥�+234 806 812 5769鈥�: *KASHE FITILA*馃挕8 *Batul Mamman*馃挅 A kwanakin da suka biyo baya Gimbi ladabi take yiwa Awaisu sosai. Tsakanisu tamkar wani abu bai faru ba. Tarewarsu a sabon gidan da ake jiran sai bayan babbar sallah idan sun dawo daga hajji kuwa tuni ta rushe. Kusan duk abin da suke bukata daga tsohon gidan sun gama kwashewa. Gimbi ta gyara dakin da Maamu zata zauna tamkar wata amarya. Dayake komai sabo ne idan ka shiga kamar kada ka fita. Dakin Daula da taci burin gyaransa ma saboda tilon 'yarta sai da ta matsawa Awaisu aka karo wani gadon a matsayin na Rumana. Karshe ta yiwa Maamu da Rumana dinki kala biyar biyar ta kawowa Awaisu. Shayi yake sha yana duba wasu takardu ta kawo ledoji manya biyu ta ajiye tare da durkusawa a gabansa. "My dear ga tawa 'yar gudunmawar" Daya daga cikin ledojin ya bude. Kaya ya gani a dinke duka super holland har biyar. Ya kalleta da alamar tambaya. Rausayar da kai tayi tana kifta idanu alamun zata yi kuka. "Nasan babu wani abu da zanyi ya wanke wautar da nayi maka kwanakin baya. Amma don Allah ina mai sake neman afuwarka. Na tsorata ne da jin labaran zama da surukai har naso bata aurena akan labaran wasu da nake ji" Tayar da ita yayi sannan ya matsa yadda zata iya zama kusa dashi. Ya kama hannunta ya rike. "Bazanyi miki alkawarin cewa kullum cikin zaman lafiya zamu kasance ba idan Maamu tazo. Amma ina so ki sani ba wai don ita ta haifeni ba, Maamuna bata da rigima ko kadan. Mace ce wadda yanayin kaddarar rayuwa ta sanya mata mugun hakuri da kawaici. Ina jin ba domin Baaba ba da a sangarce ma zan tashi saboda tsabar hakuri irin nata. Tabbas banji dadin abin da kika yi ba amma na hakura. Da kinsan yadda nake mafarkin zama inuwa daya da ita nasan baza kiyi waccan maganar ba tun farko" Sake bashi hakuri tayi tana kuka da alkawarin gyara kuskurenta ta hanyar bin Maamu sau da kafa. ***** "Anti Bebi lokacin tafiyarmu sai kara matsowa yake fa. Ni wallahi bana son yin tafiyar da mutanen nan. Dukkaninsu babu wata alamar wayewa. Muje airport su janyo a rinka kallona" Dariya sosai Anti Bebi tayi sannan ta soma magana da shakakkiyar muryarta wadda tsabar gayu da make murya wurin janyo hankalin maza ta koma haka "Ki samu ya barki muje wurin da nake fada miki. Kuma kiyi a hankali kada uwarki taji labari. Kinsan dai ba shiri muke da ita ba" Gimbi ta tsuke baki jin an zagar mata uwa. Ita kanta bata fiye shiga sabgar Antin tasu ba sai da wannan abin ya faru. Yadda Anti Bebi da Mama basa kama a fuska haka suka bambanta a hali. Yanzu haka aurenta na shida kenan. Abin mamaki masu kudi take aure suyi ta mata bauta. Sai ta tara abin da ta tara ta nemi sanadin da zasu saketa. Mama ta gaji da fada da nasihar ta tsame hannunta daga lamuran kanwar ta ta. "Shi kuma mijin naki ki barni da shege, idan Wangesi na tsangaya ya fara aiki akansa ina fada miki sai juya alkalami yafi miki wahala akan yadda zaki rinka juya shi son ranki. Shi din banza..." Mikewa Gimbi tayi tana rataya jaka rai a bace. Anti Bebi tace "Me aka yi kuma zaki tafi muna magana" "Haba Anti, zamana a nan kin zagar min uwa kin koma kan mijina. Ina sonsu bazan jure zaginsu da kike yi ba" Dukan cinya tayi irin na matan da suka ga jiya suka ga yau. "Karyar banza, Amina dai zan yarda kina sonta tunda ita ta haifeki. Amma indai Awaisu ne karya kike yi Gimbi. Duk matar da take son mutum take kin iyayensa ko 'ya'yansa na wani auren kallon munafuka nake yi mata. So da ya amsa sunansa shine ki rungumi duk abin da mijinki ya nuna yana so ki taya shi ririta shi" Ganin Antin tana ya6a mata magana ta fice ko sallama babu. Dama can ba wai tana ganin mutumcinta bane. Tun suna yara sun san tayi kaurin suna a dangi saboda fitinarta. Yanzu ma dole ce ta kawota. Zata nemarwa kanta mafita. ***** Bayan kwana biyu Awaisu yake sanar da ita cewa nan da sati uku su Maamu zasu taho Abuja domin ta nan zasu tashi. Kuma an kusa fara dibar alhazai. Sanan za'a taho da Rumana tun yanzu domin taya Laminde zama da su Haris da kuma sabawa ita ma da gidan. Da murnarta ta dauko takarda tana yi masa list na abubuwan da take so a karo musu na kayan abinci da kayan masarufi domin tarbar baki. Yadda take yi masa dole duk wani sauran zargi da bacin rai da yake ransa ya kawar dashi. Bayan ya fita a gigice ta kira Anti Bebi har ta manta abin da ya faru tsakaninsu. Ita kuwa tana ganin kiran taki dauka. Sai da ta kira yafi sau biyar sannan ta amsa tana magana da kyar wai ita a dole anyi mata ba daidai ba. Gimbi bata yi fushi ba ta fada mata yadda suka yi da Awaisu. Anti Bebi tace idan zata iya ta je ta sameta a gida washegari su tafi wani kauye a Nasarawa state inda Wangesi na tsangaya yake. Da daddare kuwa ta karantawa Awaisu karya da gaskiya saboda kada ya ga bata dawo gida da wuri ba daga bankin da take aiki. Shi kuwa sanin yanayin aikinsu bai kawo komai a ransa ba sai addua da yayi mata. Washegari tana zuwa wurin aiki tayi karyar ciwon ciki ta samu manaja ya yarje mata komawa gida. Daga nan bata zame ko ina ba sai gidan Anti Bebi. Ko zama batayi ba suka kama hanya. Dreban Anti Bebin ne ya kaisu. Tayi mamaki sosai yadda taji suna hirar malamin tsibbun tare dashi. Ashe shine ya hadasu ma. ***** Wangesi ya bata layu da guraye da zata saka a cikin gidan wanda su Maamu suna zuwa zata ji ta tsani gidan saboda zafin da zaiyi mata. Saboda yarda da shirkarsa da yayi har alkawarin dawo mata da kudinta yayi idan Maamu ta iya kwana uku a gidan batare da ta matsa a mayar da ita Fika ba. Gimbi murna ba'a cewa komai. Tana zuwa gida tayi duk yadda yace ayi da kayan da ya bata ta zauna jiran lokaci. Ranar da zasu zo ta kama asabar. Tun kafin asuba ta farka ta shiga kitchen tana ta dafa kayan tarbar baki. Laminde ma a nan ta sameta. Awaisu kuwa zuciyarsa fes ganin ta sake tana nuna masa ta fishi murnar zuwansu. Dama dreba ya tura aka dauko su. Motar na shigowa yaran suka fita a guje suna murnar ganinsu. Haris tamkar ya shige cikin Harisu don murna. Ba karamin son kawun nasa yake yi ba. Maamu ce karshen fitowa daga motar. Kafar dama ta fara saukewa cikin sanyin muryarta tace "Bismillah tawakkaltu alallah" *KASHE FITILA*💡9 *Batul Mamman*💖 Awaisu da yaransa duk da murnarsu suka koma cikin gidan tare da su Baaba. Maamu ce karshen shigowa. Ta tsaya a waje ta karewa gidan kallo. Yau danta wanda ko rabin fuloti bai mallaka ba shekarun baya da suka wuce shi ne da dankakaren gida irin wannan. Addua tayi sosai ta neman tsari da kariya gareshi da zuri'arsa da kuma sanya albarka ga samunsa. Sai da ta gama ta shigo ciki. Nan ta tarar da su Baaba Hure suna ta kalle kallen gida su ma suna yabawa. Kayan abinci Gimbi da Laminde suka rinka fitowa dasu suna jerawa a tsakiyar katon kafet din falon. Sai da ta gama sannan tazo ta durkusa har kasa tana gaishesu tana satar kallon fuskar Maamu. Wangesi dai yace gidan zafi zaiyi mata da kanta zata nemi a mayar da ita inda ta fito. Wani murmushi tayi sannan ta cigaba da tambayar Rumana yaya mutan gida. Da yake Maamu banda amsa gaisuwa da kalmomi kadan ita ba Hausa ta iya ba shiyasa bata shiga hirarsu sosai. Baaba ma yau da gobe tasa Hausarta sai a hankali, ta iya amma sai ka zata ba bahaushiya ke magana ba. Haka Rumana da Zakiyya su duk da sun dan iya amma ba kamar Awaisu mai auren bahaushiya da kuma Harisu dan kasuwa ba. Bolanci yafi kama bakinsu. Hirar dai aka ake yinta wani abin sai kaci dariya. Idan kaga Gimbi a tsakiyarsu sai ka rantse ko goyo suka nema zata yi musu. Shiyasa basu taba korafi akan ta ba. A ganinsu yanayin aiki ne yake sawa bata zuwa Fika sosai. Dakin da aka tanadarwa Maamu nan Baaba tayi masauki tare da Zakiyya. Gado ne kato wanda zai ishi mutum hudu ma. Ba karamin kashe kudi Awaisu yayi ba. Harda tv ya saka mata da fridge. Baaba da aka soke zuwanta Abujan itama yayi shirin sake gyara mata nata dakin kafin su dawo daga Hajji. Ranar a wurinsu ya yini shi da Harisu. Da safe zai tafi aiki ya bar sallahu cewa drebansa zai dawo sai ya kai Harisu kasuwa ya ga shagon nasa. Kwananusu biyu babu wata matsala da ta taso. Ranar laraba Awaisu zai tafi aiki Gimbi take sanar dashi ta dauki hutu na tafiya Hajji. Ya nuna mata jindadinsa tunda ga baki dama a gidan. Bayan fitarsa bai dade ba Anti Bebi tazo. Da yake safiya ce babu wanda yasan tazo ta shige dakin Gimbi. Mayafinta ta cire wanda ya bayyana siraran kitson da akayi mata da karin gashi. Dama ita da wuya tasa dankwali. Dan mayafi ne guntu shara shara kullum take fama dashi. "Ke kuma sai naji ki shiru babu wani jawabi game da bakinki?" Gimbi ta tabe baki "hmmm Anti wannan anya ba kudina yaci ba. Kullum naje dakin sai tayi ta murmushi babu alamun ta soma gajiya da gidan. Ita fa fuskarta kullum a sake kamar mara lafiya. Har tunani nake ko aljanun nan ne masu sa dariya basuyi mata kamu sosai ba aka tsaya a murmushi" Dariya sosai Anti Bebi tayi "Shegiya Gimbi, ashe kema baki da mutumci, yarinya tayi gadon uwa. Kuma ina mai tabbatar miki indai zakiyi yadda nake yi to babu wanda ya isa ya taka ki" Gimbi shiru tayi. Idan da Mama zata ji abin da take yi yanzu Allah kadai Yasan fadan da zatayi mata. Balle kuma Alhajinsu da ya dauki son duniya ya dorawa Awaisu. Shi a ganinsa ba karamin dace yayi da surukai ba. Sai bayan azahar Anti Bebi ta dauki mayafinta "Tashi muje na ga bakin naki sai na wuce daga can. Idan anyi sati babu chanji da kaina zan koma wurin Wangesi" ***** A falo suka tarar dasu harda su Haris sun dawo sun tsaya basu labarin makarantarsu. Anti Bebi kallo daya tayi musu taji babu wanda yayi mata a cikinsu. Duk da cewa zata yi sa'ar Ummu kulsum 'yar Baaba Hure ta uku domin ita ce autarsu Mama amma daga tsaye ta dan dago musu hannu "sannunku" Zakiyya ta amsa mata tana yi mata wani irin kallo. Wannan mata duk inda ta fito akwai rashin kamun kai a tattare da ita. Labaran da akeyi a tashar NTA Hausa shine ya dauki hankalin Baaba Hure ga Rumana ta biyewa su Amir suna ta hayaniya. Remote din tv ta dauka zata karo sautin yadda zata ji jawabin mai kawo rahoton. Tana cikin dannawa Anti Bebi ta kwashe da dariya "Mhmmm ashe harda su kaza a cin danko. 'Yata kinyi sa'a su o'o hannu baya gani ya kyale. To gaskiya a dage a sayo musu computer" Baaba Hure ji tayi kamar an zuba mata ruwan zafi saboda yadda zuciyarta ta harzuka. Bata bukatar wani bayani tasan cewa da ita wannan bakuwar take. Ajiye remote din tayi jikinta babu kwari tana jiran amsar da Gimbi zata bayar sai ji tayi tace "Waya ga dan wake a hotal" Zakiyya da Maamu sai dan murmushi sukeyi. Ita Zakiyya duk da tana dan jin Hausa ko kadan bata fahimci inda zancen nasu ya dosa ba balle kuma Maamu. Baaba Hure ganin haka itama sai ta biye musu tana murmushin. A iya saninta Gimbi bata san cewa ita asalin bahaushiya bace. Kuma yanayin da Hausarta ke fita da wuya ace tana gane karin magana indai ba yarenta bane. Gara ta nuna musu itama bata ji ko don ta ga iya gudun ruwansu. A lokaci daya kuma tausayim Maamu ya cika mata zuciya. Ashe Gimbi ba son Allah da Annabi take yi musu ba. Indai hakane kuwa akwai matsala wannan zaman da zata yi a gidan. Da yamma da Harisu da Awaiau suka shigo. Baaba taso ta sanar da Harisu abin da taji sai kuma tayi tunanin kada ta zama uwa mai sa ido. Daga faruwar abu daya bai kamata ta yanke hukunci akan cewa Gimbi ba mutuniyar arziki bace. Hakan yasa ta fasa cewa komai. ***** Bayan kwana hudu aka kirasu sune diba na biyu. Awaisu da drebansa sukayi mota biyu aka kaisu Airport. Basu dawo ba sai da jirginsu ya tashi. Madina suka fara wucewa. Tun a hanya Gimbi ta soma zazzabi mai zafi da amai. Suna isa aibiti aka kaita likita yace taci wani abu ya bata mata ciki. Duk rashin kirkin da taso gwada musu sai ta koma abar tausayi suna jinyarta. Kwanakin Madina kaf bata ji dadinsu ba. Haka suka je Makkah can ma bata da wani kuzari. Wannan Hajjin dai bata ji dadinsa ba kwata kwata. Daga zazzabi ya warke sai mura mai zafi da ciwon wuya. Haka sukayi kwana talatin suka dawo da ita duk ta fige sai mugun nufi a zuciya. ***** Sai da sukayi sati da dawowa sannan suka koma Fika aka bar Maamu da Rumana. Gimbi ce ta samar mata makaranta wadda bata da nisa sosai da gidansu. Makaranta ce mai tsada mai kyau don kawai ta burge Awaisu. Da taga hankalinsa a kwance yake da abubuwan da take yi ta koma gidan Anti Bebi tana korafin rashin aikin maganin Wangesi. "Kwantar da hankalinki naje na same shi. Yace wannan magani ranar da suka je gidan wani abu ya bata sihirin da yake ciki." Wata leda ta dauko ta mikawa Gimbi. "Ga wannan yace ki dafawa mijinki abinci dashi. Daga ranar a hankali duk wani so da kulawa da yake yiwa uwar tasa zai fara fita daga zuciyarsa. Sai kiyi amfani da wannan damar ki gasa mata aya a hannu. Da kanta zata kwashi kafarta ta gudu gashi an daure bakin" Karba tayi jindadi ya bayyana a fuskarta "Ina fata wannan karon a dace. Idan ba haka ba kuma zanyi maganinta da kaina. Shiru shirunta irin na munafukai shi nafi tsana. Kinsan irinsu abin tsoro ne. Ga wannan yarinyar da suka zo tare mai cin tsiya. Ina tsammanin horon yunwa zan fara yi musu a gidan" [4:19PM, 2/18/2018] ‪+234 803 369 4017‬: *KASHE FITILA*💡10 *Batul Mamman*💖 Ranar laraba da daddare Gimbi da kanta tayi girki sabanin yadda ta saba saboda yanayin aikinta Laminde ce take yi. Maganin da aka karbo mata ta juye shi tas a miyar Awaisu ta kara maggi. Da ya dawo dakin Maamu ya fara zuwa ya gaisheta tare da zama zai fara hira ta dube shi duk da alamun gajiya a tare dashi "Ka tashi kaje kaci abinci ka huta na yafe hirar nan" "Maamu ni sai kiyi ta korata. Da Yaya Harisu ne ai sai kin gama sauraronsa" "Sannu baban kishi. Yanzu dai ka tashi, ka ga matarka itama ba zama take yi ba. Dan lokacin naku kuma bazan so na hanata sakewa ba. Ni ban zo gidan nan don takura muku ba. Abokan hirar nawa ma abinci suka tafi ci. Yanzu zaka ga sun dawo" Tashi yayi rike da coat dinsa a hannu yace zai dawo bayan yaci abinci yayi wanka. Har ya fita tana cewa ta yafe hirar yau. Wanka yayi Gimbi ta biyo shi da abincinsa daki wai falon hayaniya tayi yawa. A haka tana yi masa hira ya cinye tuwon da ta zuba masa harda neman kari. Dadi ya kamata kuwa. Yanzu abin da ya rage kawai shine ta fara gwada aikin maganin. ***** Washegari saboda fitarsu aiki da zuwan yara makaranta tun asuba suke tashi ranakun aiki. Kitchen ta shiga ta aunowa Laminde shinkafa sannan ta fito da kazar da ta tafasa tun dare. "Kiyi min jallof din shinkafa taji alayyahu da busasshen kifi. Wannan kazar kuma pepper chicken nake so kiyi. Kiyi komai cikin sauri kinsan Abbansu Daula baya son jira." Laminde ta gyada kai "To Hajiya, amma shinkafar bazata ishemu har su Hajiya Babba ba da 'yan makaranta" Gimbi ta koma store din da yake cikin kitchen din ta dawo rike da wata karmasasshiyar doya. "Shinkafar ki dafa mana ni da yara da babansu. Wannan doyar kuma fate zaki yi muku ke da sauran mutan gidan" Laminde ta kalli doyar ta kalli uwargijiyarta. Ita dai tunda take a gidan ba'a taba yi mata wulakanci akan abinci ba. Wani lokacin ma ita Gimbi take barwa zabin abincin da za'a dafa. Kasa shiru tayi ta dan rausayar da kai tana kara kallon doyar da ta bushe "Wai Hajiya nace ba, uhmm ita Hajiya Babba nake nufi ki karo shinkafar saboda ita" Daure fuska Gimbi tayi "sunanta Maamu ba Hajiya Babba ba. Wannan so kike yi wani yayi zaton ni da ita uwargida da amarya ne. Anyway, itama faten zaki zuba mata naji ance tana son doya. Ga langa can da na karbo wurin Mama. Kinsan mutanen da suna son komai irin na zamaninsu. Shine na nace har sai da Mama ta bani cikin nata tun na aure. A ciki zaki rinka zuba mata abinci. Kuma kiyi sauri tare zamu fita zan aike ki" Kasa hadiyar yawu Laminde tayi domin tsananin mamaki. Langa ce da gaske ga kuma doya da akace ta zuba mata. Ko ita da take aiki yau tasan anso wulakanta ta bare uwarmiji. Magana take son yi amma sam bakinta ya kasa hada kalma ko daya. Tana ji Gimbi tace ita zata yi musu nasu girkin wanda suke tafiya dashi wurin aiki yaran kuma suje dashi makaranta. Ita kuma tace tayi sauri tayi faten kada su makara. ***** Rumana cikin sauri ta gama shirinta tsaf saboda bata so a jirata. Tun fara zuwa makarantarta kwanaki biyu da suka wuce tare suke fita da yaran gidan da Gimbi. Dreba ne yake kaisu makaranta ya wuce da ita wurin aiki. Tunda a banki take shiyasa suke yin sammako sosai. Ko da ta fito falo Mu'allim ne kawai Gimbi take bashi abinci a baki yana ta rigima shi bacci yake ji. Har kasa ta durkusa ta gaisheta sannan ta nufi dinning table inda kayan tea suke zata hada. "Dakata Rumana me zakiyi a nan?" Murmushi tayi ta kirata yadda yaran gidan suke kiranta "Mummy tea zan sha kafin su Haris su fito" "Kinga daga yau ki rinka zuwa wurin Laminde ki sha tea din a can." Bata ji komai a ranta ba tayi hanyar kitchen. Sake dakatar da ita Gimbi tayi "Kiyi sauri kisha ki fito kada ki makara" Dayake bata san sunan dreban ba sai tace "Mai kaimu makarantar har yazo ne? Bari na fadawa su Amir suyi sauri su ma" "A'a kina jina ko Rumana, makarantarku ba wani nisa gareta ba. Ki rinka shiryawa da wuri kina tafiya. Tafiyar da mukeyi da ke tasa ina makara kwana biyu. Gashi ba'a gama abinci ba. Idan kin dawo sai ki ci. Tea din ma ruwan zafin aka juye a girkin sai an dafa wani" Sai a lokacin Rumana taji wani iri a ranta. "To Mummy bari na tafi, sai kun dawo" Gimbi harda murmushi "yauwa Rumanan Abba. Allah Ya kiyaye kinji." Rumana ta dan tsaya jim ko zata bata kudi tunda sai hudu da rabi suke tasowa. Gimbi ta fahimci dalilin tsayuwar ta dan sake fuska "ko akwai wani abu ne Rumana?" "A'a babu komai. Na tafi" Fita tayi tana tafiya a hankali. Allah Yasa makarantar a bakin titi take kuma babu wuyar ganewa. Tafiyar minti shabiyar zata kaita idan tayi sauri. Iyayenta ne suka fado mata a rai taji kamar ta fashe da kuka. Bata san yadda zata fassara abin da Gimbi tayi mata ba. Tayi kamar minti biyar tana tafiya taji mota ta tsaya a gefenta. Horn da akayi yasa ta kalli motar. Mace ta gani tasha lullubi sai wata yarinya mai uniform irin nata. Da ta sake kallonta ta tuna ajinsu daya duk da bata san sunanta ba. Gaishe da matar tayi cikin hausarta. "Shigo mu karasa kin fito cikin sanyin nan ko rigar sanyi babu. Kada kiji tsoro ga Yusra ajinku daya tace min" Bayan motar ta shiga ta sake gaisheta sannan Yusra ta juyo "Sunanki Ummu Ruman Abali ko" Rumana ta gyada kai tana murmushi. Hira uwa da 'yar suka cigaba da yi har suka iso kofar makarantar. "Umma baki bani kudin break ba fa" "Yusra bana son wannan kashe kudin da kike son koya. Ga abinci nan a jakarki" Yusra ta sake kwantar da kai "Umma ko hamsin ce saboda siyan ruwa" Dari biyu maman ta mika mata "gashi ku raba da Rumana idan kun fito. Allah Ya bada sa'a" Rumana tayi mata godiya suka jera cikin makaranta tare da Yusra wadda take yi mata tambayoyi akan makarantar da ta baro. Da haka ta manta da bacin ran da ta fito dashi. ***** Duk sun gama shiri sun fito Awaisu ya tambayi ina Rumana. Gimbi tace "Ta tafi, wai makarantar babu nisa zata rinka tafiya da kanta." Bai ce komai ba suka fice saboda ya leka Maamu tana bacci. Bata farka ba sai karfe tara da kusan rabi. Sabanin yadda ta saba ganin tray din abincinta na safe yau babu komai a wurin sai wata langa da cokali makale a hannunta. Bata kula ba ta shiga bandaki tayi wanka. Sai da ta gama shirinta ta zauna shiru Laminde bata kawo abinci ba. Fita tayi falon taji gidan tsit alamun ita kadai ce. Komawa dakin tayi tana tunanin ina Laminde taje haka. Dama ita take tayata hira kafin yaran su dawo daga makaranta. Langar ta sake kallo bayan ta koma sai ta bude. Faten doya taci karo dashi yayi wani baki ya cure wuri guda saboda rashin wadatar mai. Haka aka yi shi kandas sai kan sauran kifin da Gimbi tayi musu abinci. Mayarwa tayi ta rufe zuciyarta tana karyata cewa wannan abincin nata ne. [4:19PM, 2/18/2018] ‪+234 803 369 4017‬: *KASHE FITILA*💡11 *Batul Mamman*💖 Haka Maamu ta zauna har azahar bata ci komai ba ga yunwa tana ji. Tasan dai wurin biyu da rabi yaran suke tasowa daga makaranta. Kila su dawo tare da Laminde. Da wannan tunanin ta cigaba da zama har uku ta wuce. Karfe daya da rabi dreba ya kira wayar Gimbi ya sanar da ita zai je dauko su Haris. Ta umarce shi da idan ya daukosu ya taho dasu bankin su jira har ta tashi. Da farko wurin Mama tayi niyar cewa ya kaisu. Sai ta tuna zata iya cewa me ya hana su koma gida saboda Islamiyya. Ita kuma ko tana hauka bata jin zata taba tura yaranta gidan Anti Bebi. Ita din ma da take zuwa yanzu don biyan bukatar kanta ne kawai. Shi dai dreba sai mamaki yake yi amma haka nan ya dawo cikin banki ya sami inuwa yayi parking. Nan fa daga mai kiran fitsari sai mai jin yunwa ko bacci. Haris da ya fisu hankali korafin rashin zuwa islamiyya yake yi. A haka suka yi ta zama har bacci ya kwashesu. ***** A makarantarsu Rumana kuwa da break sai ga Yusra tazo ta bata naira dari kamar yadda Ummanta tace su raba. Da kyar ta karba duk da cewa yunwa take ji. Yusra tayi mata tayin abinci taki karba shima. A ganinta basu yi sabon da zata ci mata abinci ba bayan ita bata zo da nata ba. Karfe hudu da rabi suka fito ta nufi titi za ta tsallaka. Yusra ta dakatar da ita "Rumana ki jira Umma tazo. Yanzu za ta biyo idan ta ajiye kannena a islamiyya" "Idan na tsaya za'a yi min fada a gida." Daga haka suka yi sallama ta tsallaka daya gefen ta kama hanyar gida. Tafiya ta rinka yi tana jan kafa saboda tsabar yunwa. Yau da azumi take yi ba karamar wahala zai bata ba. Daren jiya tun takwas da rabi tayi bacci ko abincin dare bata ci ba. Gashi yau bata samu ko ruwa ta sha ba. Da sallama ta tura kofar falon sai dai babu alamar akwai mutane a gidan. Dakin Maamu ta wuce. Tana taba kofar dakin Maamu tayi saurin tura langar faten karkashin gadonta. Tsoronta kada Rumana ta gani har wani yaji ayi tunanin Awaisu ko matarsa basa sonta ne. Zata yi bakin kokarinta wurin kare mutumcinsu a idon duniya. Takalmi kawai Rumana ta iya cirewa ta fada kan gado tana rike ciki. "Maamu yau naji yunwa sosai har jiri ya rinka daukana a hanya" Tasowa Maamu tayi ta dawo kusa da ita ta zauna tana dora hannu a kan Rumana "Baki da lafiya ne kika ki cin abinci?" Bata boye mata komai game da yadda sukayi da Gimbi ba da safe. Hatta kudin da Umman Yusra ta bata sai da ta nuna mata domin ko kwandala bata kashe ba. Hakan ba karamin daga mata hankali yayi ba da kuma neman tabbatar mata da zargin da take gudun dorawa iyalin Awaisu. "Tashi ki je ki hada shayi ki sha kafin su dawo. Doya aka dafa ke kuma nasan ba kya ci" Rumana ta yamutsa fuska saboda yadda ta tsani doya. Falo ta koma sai dai babu kayan tea a tsakiyar dinning table kamar yadda ta saba gani tun farkon zuwanta. Ta shiga kitchen nan ma babu wani abin kirki sai ta tafi zata dauko indomie a store. Nan fa taji kofar a rufe. Tunani ne ya isheta game da sauyin da ta gani a gidan yau. Haka ta koma wurin Maamu ta fada mata. Hankalinta ya sake tashi sosai. Duk da tana jin yunwa itama amma tausayin Rumana ne ya kamata. A ranta tana adduar Allah Yasa ba wani sabon salon zama zasu koma yi da Gimbi ba. Da wane ido zata kalli su Baaba Hure. "Dauko wayata ki duba nambar Gimbi ki kira" Rumana ta aiwatar da abin da aka sata. Tana zaune Maamu tana fada mata abin da zata ce a wayar. ***** Zaune take tana cike wasu takardu taji waya. Tana dubawa ta gane numbar Maamu ce. Tsorata tayi ta kasa dauka sai a karo na biyar ta dake zuciyarta. Muryar Rumana taji ta gaisheta sannan tace "Maamu ce tace na kira wai yau lafiya kuwa. Ko wani abin ya faru?" "Kice mata babu komai nima na kusa tasowa" "Su Haris basu dawo ba har yanzu sannan ni da Maamu bamu sami abinci ba. Shine tace ko zaki fadi inda key din store yake" Maamu daga gefe tana 'yar dariya tace "yau zanyi musu girkinmu don dadi duk wanda yaci sai ya manta hula da takalmi" Itama Rumana duk da yunwar da take ji jiki babu karfi dariyar tayi tana fassarawa Gimbi abin da Maamu ta fada. Shiru tayi ta kasa bata amsa daga baya ta fara cewa "hello, Rumana bana jinki." Daga haka ta kashe wayar ta cigaba da harhada kayanta a jaka. Tunaninta daya kada aikin ya baci ta sami matsala da Awaisu. Ta san yadda yake son Maamu da su Baaba. Tsoro ne sosai ya kama ta. Lokacin da ta fito shida saura ta fake da cewa dreban ya sha fama da rigimar yara ta sallame shi. Duk sun bata motar da abincin da ta bayar da kudi aka siyo musu a wani gidan abinci mai tsada na kusa da bankin. Gidan Anti Bebi ta wuce ta bar yaran a mota da gargadin kada wanda ya fito. Tare da maigidanta ta sameta ta gaisheshi yana ta bin ta da ido har suka shige daki ita da Anti Bebin. "Me ya faru na ganki da yamman nan ko waya babu?" Muryarta har rawa take yi tace "tsoro nake ji kada Awaisu ya sakeni wallahi. Yau baki ga abincin da na bar musu ba. Ina tsamani bata ci ba" Yadda tayi a gidan tun safe zuwa wayarsu da Rumana ta sanar da Anti Bebi. "Mtswww, ni kin bani haushi ma. Matsoraci baya zama gwani Gimbiya. Idan baki shafawa idonki toka ba a yadda nake ganin take takenta tunda har ta fara tambayar mukullin store saura tasa yayi miki kishiya ko ta rabaku gabadaya" Gimbi ta kara shiga tashin hankali "wallahi bazata yiwu ba. Awaisu da taimakon Alhajinmu ya zama mutum. Duk wannan aikin da nake yi da wahalar da nake sha dominsa ne. Babu wadda ta isa tazo mu zauna taci arzikin da bata san samuwarsa ba" Anti Bebi tayi dariya "yanzu kike magana, to kada ki damu idan kinje gida ta fadawa Awaisu kinga alamun zaiyi fada. Meye amfanin Laminde? Kafin ya fara fadan kiyi kanta da duka idan ya kama kina kuka kina cewa tana son kashe miki aure zata wulakanta miki uwarmiji. Daga nan ki dauki laifin duka ki nana mata ki sabule kanki ki koreta. Idan kin tashi neman wata mai aikim kizo zan hadaki da mai kawosu daga kauye" Sai yanzu Gimbi ta sami nutsuwa da kwanciyar hankali. Harda murmushinta ta fita suka koma gida. ***** Maamu ta kai wuya wurin bacin rai jira take yi su dawo. Bazata bari wannan abin yayi nisa ba gara Awaisu ya taka burki idan ma bisa kuskure ne a tunaninta ya kamata da wayar ta katse lokacin da suke magana da Rumana ta sake kira. Shirun da suka ji har Rumana ta sake kira wayar a kashe shine ya bata mata rai. Gimbi na shiga gida ta tarar da Awaisu shima shigarsa kenan. Yana son tambayarta inda ta tsaya kuma ga yara da kayansu tun na boko ya ga Maamu ta fito. Kana ganinta yau babu wannan fara'ar wadda da wuya ka ga fuskarta a hade. Jikinta gabadaya babu kwari saboda yini da yunwa. Ruwa kawai suke sha ita da Rumana. "Yanzu nake shirin shigowa dakin naki" cewar Awaisu yana matsawa kusa da ita. "Na hutar da kai. Dama nace ko kun manta damu a gidan ne yau baku ajiye mana abinci ba" Dayake da yarensu take magana Gimbi duk ta tsargu. Kallon Gimbi yayi "garin yaya kika fita ba'a ajiyewa Maamu abinci ba? Ina Laminde?" Hantar cikin Gimbi ta kada ta fara in'inar da bata san tana da ita ba "uhmm-dama-da-fate-eh faten doya aka yi mata kafin-kafin mu fita" Maamu sarai ta fahimceta sai kawai ta koma dakin ta dauko langar faten doya. A harzuke take sosai ta bude a gaban Awaisu, har wani ruwa ruwa ta fara ga baki da tayi sosai "Wannan abincin zamu ci Awaisu?" Yadda tayi maganar muryarta ta karaya domin kuka ne yake barazanar kwace mata saboda takaici. Ko aiki take yi a gidan aka bata wannan abincin tabbas anso cin mutumcinta ne. Dagowa yayi da zafinsa zaiyiwa Gimbi fada. A lokacin ba karamin tsoro ne fal a zuciyarta ba sai ta tuna hudubar Anti Bebi ta daure fuska. Kamar anyi ruwa an dauke haka ya hadiye fushinsa ya koma yana kallon Maamu. "Ai kuwa da gani faten nan zaiyi dadi. Gimbi ko zaki dumama mata a microwave yadda zata ji dadin ci" Duk da tayi mamakin saurin sauyawarsa amma saboda tana son tabbatar da aikin Wangesi tace "to my dear, dan tambayar min idan tana son manshanu sai na saka mata ma. Kasan Laminde gwanar girki ce" Haka kuwa ya tambayi Maamu hankali kwance. Kasa bashi amsa tayi saboda a take a lokacin wani irin abu taji ya soki zuciyarta. Tana kallo Gimbi ta wuce kitchen da langar wai zata dumama ta dawo mata dashi. Awaisu kuwa yana murmushi yace mata zaije ya watsa ruwa yazo suyi hira. Bayan tafiyarsa Maamu ji tayi jiri zai kwasheta ba don yunwa ba sai don yadda zuciyarta ta karaya da halin da ta tsinci kanta daga zuwa gidan tilon danta abin alfaharinta. [4:24PM, 2/18/2018] ‪+234 803 369 4017‬: *KASHE FITILA*💡12 *Batul Mamman*💖 Da kyar Maamu ta kai kanta daki inda Rumana take kwance duk sauran kuzarinta ya kare. Tana turo kofar Laminde wadda babu wanda ya lura tana tsaye a bakin kofar shigowa gidan ta dafe kirji. Duk abin da akayi a kan idonta ne. Wannan abu ya kara daure mata kai har ta rasa da me za ta kwatanta shi. Ko ma menene akwai wani abu da uwar dakinta take yi game da surukarta. Tun safe da suka fita Gimbi ta aiketa kasuwa. Daga can ta ce ta wuce wurin kanwarta da aka kawosu aiki Abuja tare. Haka ta tafi cike da mamaki musamman da ta fada mata kada ta koma sai ta kirata a waya. Wayar da ba'ayi mata ba sai da ta baro gidan Anti Bebi. Gimbi ta gani ta dawo da langa tana tiriri ta dorata akan wani tray na silver kasanta kuwa duk yayi baki. "Yaushe kika dawo ban sani ba?" "Shigowata kenan" "To aje ayi min wanke wanke" Laminde tace to ta juya kitchen. ***** Bayan fitar Gimbi Maamu ko bude abincin bata yi ba ta dauka ta kai kitchen. Lokacin Rumana bata farka daga baccin yunwar da take yi ba. Tana shiga ta ga Laminde ta bude wani flask da shinkafa a ciki tana shirin zubarwa. Abincin Awaisu ne na office ko rabi bai ci ba. Maamu ta rasa yadda zata kwatantawa Laminde ta bata abincin. Can dai ta nuna abincin tace Rumana. "Rumana zaki bawa?" Maamu tace eh. Laminde ta mika mata flask din. Karba tayi ta koma daki ta tashi Rumana. Duk da tana so haka ta bar mata. Ita kuwa tana ganin abincin haka ta soma ci babu wanke hannu bare kuskure baki. Maamu na gefe sai hawaye take sharewa batare da ta bari Rumanan ta gani ba. Yarinyar da gidansu ba'a san yunwa ba itace yau ta bawa ragowa. Da Harisu zai ganta yanzu bata san inda zata saka kanta ba. Rumana ta cinye abincin tas ta sude flask din kamar almajiri yaje bara an bashi lomar tuwo uku. Tana gamawa sai amai tun a dakin ta fara Maamu ta kama ta zuwa bandaki. Tana yi tana kuka domin tun tana fitar da abinci sai da ya koma yawu kawai take zubarwa idan ya yunkuro. Haka Maamu ta gyara wurin tace Rumana ta kwanta. Babu bata lokaci wani baccin ya dauketa baki a bude. A daren Maamu tayi kuka har kanta ya rinka ciwo. A kusa da Rumana tayi bacci. ***** Bayan asuba Gimbi ta shiga dakin ta tarar da Maamu akan abin sallah ita kuma Rumana tana shafa mai. A ladabce ta gaishe da Maamu kamar bata yi musu komai ba. "Rumana jiya kika bar kanwarki ta kwana ita kadai. Ko kinfi son kwana a nan ne?" Kai kawai ta gyada don ta fara tsoron Gimbi yanzu. Murmushi tayi a ranta tace tafi nono fari. "To ai babu komai hakan ma yafi. Zaki rinka debewa Maamu kewa" Daga haka ta fice zuciyarta cike da nishadi. Yanzu zata gyarawa Daula dakin yadda ta tsara tun farko. Kitchen ta wuce ta samu Laminde har ta gama farfesun kayan cikin da ta sakata. Ta zubawa mijinta da yaranta sannan ta dauko langar Maamu ta soma zubawa. Laminde tana goge gefen gas cooker din ta saki tsumman tana kallon ikon Allah. Hanji ne Gimbi take ta za6ewa tana zubawa ya kusa rabin langar. Jikinsa duk kitse yayi wani narai narai babu kyaun gani. Kasa hakuri Laminde tayi "Hajiya nace ko kin manta wannan langar kince ta Maamu ce" Fuska a hade saboda bata son bada kofar tsawaita zancen tace ban fahimceki ba. "Na ga kina ta zuba hanji ne a ciki." "Hanjin ba nama bane? Kinga ki kiyayeni da shisshigi wallahi. Kin saka min ido ni da gidana sai nayi miki bayanin abin da nake yi. To binciken likitoci ya tabbatar da cewa cin dafaffen hanji yana matukar taimakawa tsofaffi da kara musu lafiya" Awaisu yana daga falo suna jiran ta kawo breakfast shi da yara ya jiyo muryarta tana fada. Kitchen din ya shiga "Me ya faru kuma kike fada da safen nan?" Rufe langar tayi tace "kyaleni da ita, ina jin ta fara gajiya ne da aikin" Laminde sai faman bada hakuri take yi. Ya so jin abin da ya hadasu sai dai shima bai ga fuskar tambaya ba. Yana kallo ta dauki langar tare da bread wanda ta yanka gida hudu ta dauki bari daya sai tea a kofi ta kaiwa Maamu da kanta. Bayan fitarta Rumana ta gama shirin makaranta. Duk da bata da kwari sosai amma a ganinta fitar zata fiye mata. Kafin ta fita Maamu ta mika mata dari biyu cikin kudin da Harisu ya bata wanda a lokacin tayi ta cewa ya barshi. Ashe zai musu rana. "Ki sayi abinci a makaranta kici kinji ko. Zan yiwa baban naku magana sai ya rinka baki kudi da safe ko kuma a baki abinci kema" Rumana tayi mata godiya ta fito falo. Suna zaune dukkansu suna cin abinci suna wasa da yaransu. Awaisu ta gaisar yaran suna tambayarta ina taje jiya basu ganta ba. Murmushi kawai take yi. "Zauna ki hada tea kuyi sauri kada ku makara" inji Awaisu. Gimbi ta dan juya ido "har ka manta na fada maka za ta rinka tafiya da kanta. Rumana shiga wurin Laminde kiyi brealfast kinji." "Me yasa bazata ci a nan ba?" Awaisu ya tambayeta harda dan daga murya kamar zaiyi fadan gaske. "Bana so Laminde ta ga kamar muna wareta ne. Shiyasa nace su ci tare. Banyi laifi ba ko?" Ta rausayar da kai tana masa fari. Shiru yayi yana ta auna maganar. Har ransa baiji dadi ba kuma fada yaso yi sai dai yana bude baki yaji bazai iya ba. "Bakiyi komai ba. Kuyi sauri bana so kowa ya makara" Daga haka kowa ya karasa cin abincinsa suka tashi zasu tafi. Rumana itama ta fito bayan ta gama cin nata hanjin da bread. Sai tea wanda tana sane ta tsula masa ruwa don ya kara yawa ko zata dade bata ji yunwa ba. Suna fita itama ta fito ta tafi. Yau bata hadu da su Yusra ba sai a aji. Da break ta hada da kudin da Maamu ta bata da na wurin Umman Yusra ta sayi fanke na dari da meat pie 'yan hamsin guda hudu. Yusra ta rinka kallonta, ina zata kai wannan abincin ita kadai. Meatpie daya taci da fanke biyu ta saka sauran a jaka zata kaiwa Maamu. ***** Da farko Maamu kin cin abincin tayi sai daga baya da yunwa ta cigaba da cinta ta dauki kofin tea din ta shanye. Ta bude langa sai ga hanji da romon ya daskare ya hade jikinsa. Idan jiya tana kokonto yau ta tabbatar Gimbi da gaske wulakanta ta take sonyi. Tasan karshenta gidan ne bata so ta zauna musu. To amma komai wahala zata jure. Ta cinye rayuwarta a alfarmar gidan Harisu da Baaba Hure. Yanzu kuwa da kunya ta koma. Idan ta koma din ma ace nata dan ya kasa riketa. Shawara ta yankewa zuciyarta idan ya dawo zata ji ta bakinsa game da wannan gashin kuman da aka fara yi musu. Ko aikatau tazo yi a gidan a tunaninta bata cancanci a wulakanta ta ba. Sai yanzu take kara godewa Allah da aka ki yarda su zo da Baaba. Da bata san da idon da zata kalleta ba don kunya. Haka nan ta rinka cin hanjin tana hawaye. ***** Da rana Laminde bata kawo abinci ba zuwa da tayi suyi hira. Duk da ba komai take fahimta a zancen ba amma tana jindadin yadda take mutumtata. Rumana tana dawowa ta dauko abincin jakarta suka ci ita da Maamu. Wannan abu ya tsayawa Maamu a rai sosai. Bakinciki yasa ko fanken hannunta bata gama ci ba ta ajiye. Sai karfe shida su Gimbi suka dawo. Yau ma yaran basu je islamiyya ba. A lokacin ta bude store ta mikowa Laminde semovita tace ta dora tuwo. Cikin sauri tayi ta gama domin itama ta horu da yunwa. Gimbi da kanta ta raba abincin ta zubawa Maamu tuwo da miya a hade. Rumana itama a plate aka hada mata ta ajiye a kitchen. A haka suka kwashi sati biyu tana musu kisan mummuke sannan tana auna karfin mulkinta akan Awaisu. Da ta tabbatar aiki yayi kyau ne ta kira Anti Bebi akan tana son na mallaka domin tun a haka tana ganin yadda baya iya yi mata musu ko kadan. [4:28PM, 2/18/2018] ‪+234 803 369 4017‬: *KASHE FITILA*💡13 *Batul Mamman*💖 Anti Bebi ta rinka yiwa Gimbi dariya " 'yar gari waye ya fada miki haka nan mata suke zaune, duk wadda tace miki bata dan lekawa wurin neman taimako domin samun zaman lafiya a gidan aurenta karya take yi. Abin da naso uwarki ta fahimta kenan sai ta rinka gayamin maganganu" Gimbi na jin haka ta daure fuska "nifa kinga abin da yake hadani dake kenan, akan zagin Mama fa sai naci..." shiru tayi sanin cewa yanzu sirrinta a tafin hannun Anti Bebin yake. "Karasa mana mara mutumci. Ni zaki zaga Gimbiya. Lallai wuyanki yayi kauri. Yadda na kaiki wurin Wangesi akan mijinki kinsan ba karamin aikina bane na koma akanki ko" Gaban Gimbi ya fadi a tsorace ta soma bata hakuri. Sai dai tana cikin magana taji ta katse kiran. Da ta sake kira kuwa a kashe taji ta. Yanzu ko da wuka a wuyanta bazata iya kwatanta hanyar zuwa wurin Wangesi na tsangaya ba. Kuma ba karamin aikin Anti Bebi bane taje tasa ayi mata wani mugun abun. A da bata gama sanin wacece ita ba sosai sai yanzu da suke tare. Ban da mijinta da ta shanye hatta mahaifiyarsu wato kakarsu Gimbi bata taba yi mata musu. Duk yadda tace haka ake bawa su Mama umarni kuma dole suyi idan ba haka ba ta nuna musu fushinta sosai. Kuma bata taba yi mata fadan abubuwan da take yi da aure aure ba. A ranar ta bita gida tayi ta bata hakuri daga karshe suka daidaita. ***** Watanni biyu kenan da shigar su Maamu cikin kunci a gidan Awaisu. 'Yar hirar da yake zuwa suyi ma sai yayi kwana biyu bata sa shi a ido ba. Ranar da ya zo kuma zai sake yayi ta bata labarai batare da kula ko tambayarta idan tana da damuwa ba. Ya riga ya sakarwa Gimbi komai da ya shafi Maamu da Rumana. Hatta kudin makaranta ko abinci da ta nemi a rinka bawa Rumana cewa yayi zai fadawa Gimbi. Sau tari ya kan tsinci kansa da tunani akan rashin dacewar abin da yake yi mata. Amma ko a bayan idon Gimbi bai taba kuskuren canjawa zuwa Awaisun Harisu da aka sani ba a gaban Maamu. Yau Rumana ta dawo da yunwa saboda dan kudin hannun Maamu tuni ya kare. Abincin rana kuwa dama an soke shi a hankali. Da safe take sawa Laminde tayi musu girki wanda take tafiya wurin aiki dashi a zubawa yaranta. Da rana tace ba zama suke yi ba Laminde ta huta. Sai biyar zuwa shida idan sun dawo a dora na dare. Kana ganinsu har sun fara rama. Idan sunyi waya da Harisu sai tayi ta kokarin danne damuwarta. A matsayinta na uwa ga Awaisu duk yadda suke da su Baaba Hure akwai abin da dole kaji kunyar fadawa duniya. Yau da wata aka yiwa haka da sauki sai ta iya shiga ciki domin tsawatarwa. Amma ita mahaifiyarsa da kanta wurin wa kuma zata kai kara. Suna zaman jiran abincin dare a dakin Mu'allim ya shigo yana buga ball. Da karfinsa ya mako ta bata fada ko'ina ba sai fuskar Maamu. Rumana ta tashi da sauri ta kwada masa mari. Dama tuni Gimbi tasa yaran suka dena shiga dakin wai bata so suna damun Maamu. Jin zafin marin yasa ya kwalla kara. Sai ga Gimbi ta shigo a guje ta dauke shi tana tambayar me aka yi masa. Yana rike da kumatu ya fada mata Rumana ce ta mare shi. Batare da neman ba'asi ba ta sauke shi a gaban Maamu tace ya rama. Rumana ta zaro idanu "Mummy kinga fa wannan katuwar ball din ya bugawa Maamu." "Shine zaki mare shi saboda mugunta bayan kinsan ba da gangan bane. Ki bari ya rama ko kuma ni na rama masa" Rumana ta kalli Maamu tana hawaye saboda irin wannan cin zarafi da akeyi musu. Idan da kara ko cin zalinsa akayi tunda Maamu tana wurin bai kamata tayi magana ba. "Gara ke ki rama masa akan na bari kanin bayana ya mareni" ta fada tana kuka Motsin tahowar Awaisu Gimbi taji ta rage sautin muryarta "Bazaki bari ya rama ba?" "Wallahi bai isa ya mareni ba" fushi da bacin ran da take boyewa ne ya fito yau. Ita bata ki ace ta tattara ta koma gida ba. Awaisu ya shigo rai a bace ganin yadda take kallon Gimbi ido cikin ido ya daga hannu zai mareta. Sai a lokacin Maamu ta tashi ta rike masa hannu. "Idan ka taba yarinyar nan zaka hadu da bacin raina Awaisu" "Maamu kada ki bari Rumana ta tashi a sangarce. Baki ga yadda take yiwa Gimbi rashin kunya bane" Gimbi dai bata jin me suke fadi da yarensu. Jin an ambaci sunanta ta matso 'yar kwalla "Abban Haris ka bar maganar nan haka. Bana so Maamu tayi fushi da kai akan wannan 'yar matsalar. Rumana kiyi hakuri kinji" Tsabar mamaki yasa ta kasa magana ma. Shi kuwa Awaisu ficewa yayi rai a bace a ganinsa sangarta Rumana za'ayi tunda tana yiwa matarsa rashin kunya kuma an hanashi hukunta ta. Da suka fita Rumana ta fashe da kuka Maamu ta kasa rarrashinta. Ita da idonta har ya kumbura ya kankance cikin dan lokaci amma Awaisu ko kula baiyi ba me zata ce mata a wannan lokacin. A haka Laminde tazo ta kawo musu tuwonsu. Dole suka ci tunda sun wuni da yunwa. ***** Kallo suke yi a falo tare da yaransu suna taba hira. Hankalin Awaisu ne ya tafi wurin Mu'allim da yake fadawa 'yan uwansa ya iya buga ball da karfi har Maamu ya bugawa a fuska. Daga kashingidar da yayi ya tashi da sauri "wa ka bugawa ball kace?" Gimbi tayi saurin tarewa "ku tashi ku tafi ku kwanta dare yayi" Awaisu ya janyo hannun Mu'allim. Fuskarsa babu alamun wasa ya tambayeshi me ya faru a dakin. Gimbi ya fara kallo sai dai bata da ta cewa a wurin. Dolensa ya fadi abin da yayi da marin da ya sha. Da sauri Awaisu ya tashi yayi hanyar dakin Maamu. Gimbi ta soma kiransa sai dai ko juyowa baiyi ba. Yana shiga ya tarar da Maamu a kwance ta rike kankarar pure water a daidai idonta yayin da Rumana har yanzu kuka take yi. Kankarar ya karba ya ga idon ya suntume. "Subhanallahi Maamu kiyi hakuri. Yanzu nake jin abin da ya faru" Tashi tayi zaune idonta cike da kwalla tace Rumana ta fita "dama irin zaman da kake son yi dani kenan ka takura muka taho?" Kansa ya sunkuyar kasa yana bata hakuri. "Yaushe rabon da ka shigo dakin nan balle ka duba lafiyarmu? Bance kada kaso iyalinka ba amma ka tuna cewa nima ina da hakki a kanka. Bana neman komai a gareka da ya wuce ka bani girman da Allah Ya bani akanka sannan ka kula da amanar Rumana. Idan ka wulakanta zuri'ar Baaba Hure kafi kowa sanin irin kallon da duniya zata yi maka. Sannan a lahira ka tashi cikin masu tozarta zumunci." "Kiyi hakuri, nasan nayi kuskure amma zan gyara in sha Allahu. Na rasa abin da yake damuna ni kaina" Duk da ranta a bace yake amma taji dadi yau ya nuna damuwarsa garesu "Ka tashi ka tafi ya wuce" "Asibiti zan kaiki saboda idon. Shi kuma zai gamu dani wallahi." A fusace ya fita daga dakin. Rumana da take tsaye a gefe yace mata daga yau ta rinka fitowa da Maamu falo suna shan iska baya son suna kulle kansu. Dakin yaran ya wuce Gimbi tana tambayarsa me zaiyi da wayar chaja bai kulata ba sai gani tayi ya fara laftawa Mu'allim dan shekara bakwai a jikinsa. Yana dukansa duk ya cika gidan da ihu Gimbi ta kasa karbar chajar sai ma rabonta data samu a baya. Maamu tana jinsu ta kwanta abin ta. Bata kin jikokinta amma ta kula da yadda suka bi sahun babarsu wurin banzatar dasu a gidan. Ranar Awaisu da Gimbi barambaram akayi babu mai kula dan uwansa tun bayan da ya gama hukunta Mu'allin tare da ja mata kunne sosai akan Maamu. Da safe a motarsa suka dauki Rumana zuwa makaranta ya bata dubu biyar yace ta ajiye sauran a gida. Yaso kai Maamu asibiti ma tace ta warke. ***** Gimbi tana fita da suka kai yara makaranta gidan Anti Bebi ta wuce. Tana kuka ta fada mata irin dukan da Awaisu yayiwa Mu'allim. Gashi tana ganin kamar maganin ya fara sakinsa. "Ni dai kawai kizo muje gidan Wangesi kada komai ya lalace min" "Gimbi kenan wato mugu baya so a dandana masa zumarsa sai ya birkice. Don yau daya anyi miki meye na fushi. Can wurin aikin naki fa?" "Ni dai kawai kizo muje zan san karyar da zanyi musu" Ko mijinta bata sake lekawa ba ta dauko dan gyalenta suka fice. Gimbi ta sallami nata dreban suka wuce da dan koran Anti Bebi. Wangesi ya bata wasu kwayaye guda hudu duk anyi musu zane da jar tawwada da wasu layu da kulle kullen magani. Komai yayi mata bayanin yadda zata yi amfani dashi ta kawo kudi ta ajiye masa. Suna komawa gida ta wuce. Kwai daya a kofar dakin Awaisu ta fasa shi ta rufe da door mat. Sauran biyun kuma daya a bayan dakin Maamu dayan kuma ta dafa shi ta cinye. Da ta gama ta dauki motarta ta koma gidan Anti Bebi sai lokacin tashin yara ta dawo. Manajan bankin da take ya kira Awaisu kan cewa yayi mata magana akan fashi da rashin zuwa da wuri ko kuma fita kafin a tashi. Don ma yana ganin kimarsa ne da tuni ya bata takardar jan kunne. Hakuri ya bashi tare da godiya. Yana dawowa ya hauta da fadan sai ta gaya masa inda take zuwa. Ta rasa amsar da zata bashi. Abincin da ta zuba rabin maganin kuma yaki ci. Daren ranar yaransa yasa a gaba suka taya Maamu da Rumana hira a falo. Gimbi kuwa Anti Bebi ta kira tana kuka Wangesi ya ci kudinta a banza. "Kin fiye wutar ciki. Haka aka ce miki asirin yana kama mutane kamar a fim? A hankali zai cinye shi ya dawo miki tamkar sakarai shashasha" Tsaki tayi ta ajiye wayar. Ita Anti Bebi bata da aiki sai fadin bakar magana. Awaisunta ba sakarai bane ta fada a zuci tana huci ita kadai. Sai bayan sati ta kula ya fara sanyi fiye da yadda yayi a baya ma. Sa idonsa akan lamarin su Maamu da suka fara shanawa yanzu babu. Gidan jiya aka koma inda take horasu da yunwa wai don kada suji dadin gidan su cigaba da zama. [4:30PM, 2/18/2018] ‪+234 803 369 4017‬: *KASHE FITILA*💡14 *Batul Mamman*💖 *Bayan Sati Uku* Zaune take gaban madubi tana kwalliya taji kamar ana kiranta. Jagirar hannunta ta ajiye ta fito daga dakin tare da leka falon ta saman bene. Mijinta ne ya shigo rai a bace sai huci yake. "Shuhada kina ina ne?" Saurin saukowa tayi har tana hada bene biyu a lokaci daya "Me ya faru T?" Mugun kallo ya bita dashi kafin yayi magana "kizo ki fice daga gidan nan na sakeki" Ji tayi kamar an sakar mata guduma a tsakiyar kanta "Ka sakeni? T kalmar saki fa ba kalmar wasa bace" Idanunsa kara rinewa sukeyi suna yin ja saboda bacin ran da ya rasa dalilinsa. "Ni zaki rainawa hankali, to zamana dake ya kare. Ki tattara ki fita kafin kiji hannuna a jikinki" Shuhada rasa bakin magana tayi. Anya mijin nata hankalinsa daya kuwa. Ya fita suna farinciki da juna. Me ya kawo wannan chanji haka. Dan matsawa tayi kusa dashi "T ka zauna don Allah muyi magana. Na rasa gane abin da yake faruwa. Abokanka sun baka wani abu ne kasha da baka sani ba?" Saukar mari taji har biyu "kina nufin ina shaye shaye ne." Dafe kuncinta tayi tana kuka "Tajuddeen kana cikin hankalinka kuwa. Nice fa, me nayi maka haka" Girgiza kai yayi yana yamutsa fuska "tsanarki kawai nayi S. And I want you to get out now kafin raina ya kara baci" Kuka ne sosai yaci karfinta. Gabadaya kwakwalwarta ta toshe. Mutum ya fita lafiya ya dawo a birkice. Ba karamin so yake nuna mata ba tun kafin aurensu har zuwa yanzu da suka sami shekara daya tare. Gani tayi ya hau sama ya fara cillo mata kayanta ta saman bene. Lallai da gaske yake. Tana kallo ya gama ya sauko ya bude wallet dinsa. Kudi ya debo ya watsa mata a fuska. "Now get out" Itama nata ran ya gama baci "babu inda zani Tajuddeen, a musulunce ma dai mace a dakinta take yin idar saki daya ko biyu. Sannan a daren nan ina kake so naje? Ba fa Nigeria muke ba inda zaka sakeni na tafi gida." Cikin halin ko in kula yace "tafi wurin kaninki" Bude baki tayi "yaron da yake hostel din maza" "Indai don ki kwana ne to na sakeki saki uku. Ai dai babu sauran igiya tsakaninmu." Karo na biyu kenan da Shuhada ta shiga tashin hankali dalilin saki. Na farko a gabanta ita da kaninta mahaifinsu yayiwa babarsu saki uku. Yau gashi anyi mata batare da wani kwakkwaran laifi ba. Jiri ne yake dibarta amma a haka ta fara hawa benen zata koma sama. Tajuddeen yayi saurin tareta yana cewa bazata kara shigar masa daki ba. Bata da kuzarin fada saboda duk abin da ya faru tamkar mafarki haka take jinsa. A sanyaye tace "wayata zan dauko da mayafi. Sannan ka bani passport dina" Saman ya hau ya dauko mata wayar da passport. Mayafi kuwa kayanta da ya watsar ya nuna mata. A nan ta durkusa ta dauka ta fita. Wani sanyi ne ya ratsa ta ga dare karfe goma da rabi. Da kyar ta sami taxi wadda ta kaita jami'ar da Suhail kaninta yake karatu a nan Singapore. Da ta sauka ta kira wayarsa tayi sa'a ya dauka a kiran farko. Tana jin muryarsa ta saka kuka mai cin rai. Nan hankalinsa ya tashi da kyar ya samu ta fadi inda take a wajen makarantar ya fito. "Sis me kike yi a nan a daren nan ke kadai?" "Ya sakeni Suhail, har saki uku." Wani kukan ta soma sai gashi ya koma babban yana ta rarrashinta. Bayan ta dan nutsu ta labarta masa abin da ya faru. "Hotel zanje na kama sannan na kira Daddy ya turo min kudi. Kaga last week ka ranci kudi a hannuna yanzu bani da enough da zan sayi ticket na koma Nigeria." Suhail ya sunkuyar da kai yana ajiyar zuciya "Sis ko kin kira bazai aiko miki da komai ba. Kudin da na ranta wurinki ciko nayi na biya kudin registration." Shuhada ta zaro ido "me kake nufi?" "Na fi wata ina cewa ya turo min kudin registration yana cewa babu. Dana matsa masa rannan sai yace wai dama ai saboda mijinki yana aiki a nan ya turoni karatu. Tunda bashi da kudi meye amfaninku. Ganin kada su dakatar min da karatu yasa na ranta kafin ya turo min sai na baki" Dafe kai tayi tana mamakin wannan abu. Tasan waye mahaifinsu a Nigeria. Babu yadda za'ayi yace kudin makarantar dansa ya gagare shi. A yadda yake ko da da gaske babu bazai taba bari su sani ba zai nemo ko bashi ne. Hankalinta ne ya kara tashi ta ce masa zata nemi wurin kwana washegari yazo ya sameta. A dakin hotel din baban nata ta kira kamar yadda ya fadawa Suhail itama cewa yayi ta nema ko ta bawa mijinta hakuri ya biya mata. Tayi kuka a daren har asuba bata runtsa ba. Da sassafe ta koma gidanta da sunan kwashe kayan sawarta. Tajuddeen ta roka ko zai biya mata kudin jirgi ta koma gida. Nan yayi mata rashin mutunci ya koreta. Dole ta kira mahaifiyarta mai fama da hawan jini ta sanar da ita. Da dan kudin hannunta take biyan hotel din. Kullum suna tare da Suhail suna shawarwari. Bayan kwana takwas mamanta tasa aka turo kudin jirgin. Filinta ta sayar domin duk wani abu na kadara da ta samu wurin babansu sai da ya karbe bayan sakin. Ana gobe zata tafi Suhail yana tayata hada kaya harda kukansa. Shekararsa ashirin da biyu ita kuma da hudu. Text ne ya shigo wayarta daga numbar da batayi tsammani ba. _Kada ki kuskura kizo min gida da sunan zawarci. Kamar yadda kika kirga min aure da na auri ubanku kema yanzu kika fara. Ke da duk wani naki baku isa ku ja dani ba_ Sai yanzu ta gane dalilin sakin da Tajuddeen yayi mata. Yadda aka raba iyayenta itama haka akayi mata. Gashi an rabasu da mahaifinsu. Bata nunawa Suhail komai ba. Sai dai ta kuduri niyar canjawa daga Shuhadar da mai shiru shiru da hakuri. Washegari da daddare jirginsu ya tashi. Uku na yamma suka sauka a Nnamdi Azikiwe Airport Abuja. Tana saukowa daga jirgin tana saka yadda zatayi maganin Anti Bebi matar babanta. ***** Gimbi na kwance a daki yau asabar tana hutawa taji waya daga Mama. Bayan sun gaisa take sanar da ita cewa ta fita unguwa ne kuma suna hanya zata biyo su gaisa da Maamu. Zumbur Gimbi ta mike daga kan gadon. Karfe biyu da rabi ko abincin da za'a dafa bata aunowa Laminde ba. Da sauri ta shiga kitchen din tana kwala mata kira. Dama tasa tayi miya tun dare. Shinkafa tace ta dafa ita kuma ta hau aikin salad. Bayan ta gama ta dauko dabinonta wanda ya kwana biyu a jike cikin fridge tare da kanunfari da dakakkiyar danyar citta ta hada da kwakwar da tasa Rumana tayi mata grating ta zuba a blender. Nan da nan ta gama markadesu ta tace ta kara madara. Kankara ta fasa ta hada a jug ta jera a tray. Bayan an gama shinkafar ta cika mata cooler madaidaiciya ga miya taji nama. Cikin awa daya sun gama komai sai jiran Mama. Abincin Maamu a langar nan ta zuba ko salad bata samu arzikin a zuba mata ba. Laminde a ranta tace lallai uwa tafi uwa. Suna kitchen din suka ji sallamar Mama. Gimbi ta kalli Laminde tana ta murna "kinsan Mama bata son zuwa gida 'ya'ya ba kamar wasu tsofaffin ba. Shiyasa kika ga na hada mata wannan. Ki biyoni da abincin nata. Maamu ki kai mata nata daki ba sai tazo falo ba" Da murna ta taro Mama suka gaisa sannan ta tashi tana rike da hannun Amir "Kinsan ba wurinku nazo ba. Kaini dakin Maamu" Yayi mata jagora har dakin. Gimbi ta koma dakinta da sauri ta sake gyarawa ta fesa air freshner sannan ta shimfida katuwar dadduma a kasa. Fitowa tayi zata je kitchen ta hango Laminde a kofar dakin Maamu da katon tray din kayan abincin Mama. Da sauri tace "Ke, ke, ke Laminde dawo" Laminde tana ji tayi biris da ita ta shige dakin. Maamu ta samu da Mama suna taba 'yar hira da kalmomin da Maamun take fahimta. Har Mama tana cewa ta rame ko kewar babban danta take yi. Laminde ta ajiye musu abincin a tsakiyarsu. Mama tayi ta korafin meyasa basa gama abinci da wuri. Maamu ta bude ido tana kallon wannan gara wadda ta manta rabon da ta ga abincin arziki irinsa. Ita kuwa Mama plate din da ta gani guda daya ta zuba musu abincin tare. Tuni idanun Maamu suka fara cika da kwalla da Mama tace mata su ci. Ita da gidan danta ta koma tamkar almajira. Mama ta rinka kara musu suna cinyewa tare. Maamu ta saki ciki taci ta koshi tasha lemon kwakwa. Rumana da take dakin ma sai da Maamu ta cika kofi taf ta mika mata. Gimbi kuwa daki ta koma tana ta kai kawo. Ta rasa wane hukunci ya dace da Laminde. Sai daga baya ta fito ta koma dakin Maamu. Laminde tana hango shigarta ta bawa Mu'allim langar abincin Maamu tace ya kai mata. Haka ya karba yana turo baki yaje ya dangwarar mata a gabanta. Mama ta daka masa tsawa "nifa shiyasa bana son wasan jika da kaka, wani lokacin sai raini yayi yawa. Abincin waye wannan duk kanzo" Maamu tayi murmushi ta mika hannu "nawa ne" Gumi ya karyowa Gimbi saboda kallon da Mama ta jefa mata. Baki na rawa tace "Mu'allim dauki ka cewa Laminde wai wa ta zubawa wannan abincin" Da yake gwanin tsiwa ne yace "Mummy langar abincin Maamu ce fa." Sannan ya fice abinsa. Maamu da yarensu ta fadawa Rumana ta ajiye a gefe zuwa anjima idan ba'a gama na dare da wuri ba sai suci. Mama ta ritsa Gimbi da idanu, ita kuwa taki yarda su hada ido saboda tasan yau me rabasu sai Allah. *KASHE FITILA*💡15 *Batul Mamman*💖 Laminde tana daga kitchen ta hango Mama a gaba rai a bace Gimbi na bin bayanta suka shiga hanyar dakinta. Rufe kofar kitchen din tayi ta kwashe da dariya. "Haka kawai kin mayar da mata almajira a gidan danta. Allah Ya budi idon Alhaji dai ya gane irin matar da yake aure" ***** Mama ko zama bata yi ba ta juyo tana hararar Gimbi. Kana ganinta ta gama tsorata sai dai kuma a yanzu jan ido bazai hanata kudirinta na ganin Maamu ta bar musu gida ba. "Gimbi me yaron nan yake nufi da cewa abincin kakarsa ne a wannan kodaddiyar langar?" "Haba Mama yanzu shine duk kika bata ranki? Har kin tsorata ni. Dambun nama ne na zuba mata a ciki kwanaki to shine suke ganinsa a dakin" Mama ta danyi jim kamar bata yarda ba "Yanzu surukar taki kika zubawa dambun nama a ciki don wulakanci. Idan nice kinsan jifanki zanyi dashi. Ko da wasa wallahi kada ki kara" Gimbi tayi mamakin saurin saukowar Mama ta bata hakuri da alkawarin bazata kara ba. Mama tace "na kula dai ba karamin ci tayiwa abincin nan dazu ba. Ki dena barinta da yunwa. Abincin rana ace sai hudu saura babu dadi" Tabe baki tayi saboda samun wuri "mhmm Mama don ba a gidan nan kike ba. Haka take wannan cin abincin. Kuma Abban Haris na dawowa sai kiji tana cewa bata ci abinci ba " "Ni dai na fada miki gara uwarmiji ta cuceki akan ki cutar da ita. Mijin da kike takama dashi aljannarsa tana tare da farincikinta dashi" Zama Gimbi tayi tana ta fadin karairayi duk tace Maamu ce take yi mata. Sai dai tana kula tamkar zancen bai shigar Mama. Suna nan ta jiyo muryar Awaisu ta tashi. Bata jima da fita ba wayarta da ta bari akan gado ta hau kara. Mama ta mika hannu ta dauko *Anti BB* ta ga an rubuta. Zata amsa kenan Gimbi ta shigo, kusan fizgar wayar tayi daga hannun Mama har ta bata tsoro. "Wata mata ce da nake bi bashi take kin daukar wayata shine ta kira yanzu." Dauka tayi tace zata kira tana tare da mamanta. Anti Bebi tana jin haka tayi dariya kawai a ranta tana mamakin Gimbi. Ita kaifi daya ce babu kumbiya-kumbiya. Gimbi kuwa fuska biyu gareta. Wato sai tana da bukata take nemanta. Zasu gamu ne. Mama abin ya kara daure mata kai yadda Gimbi ta canja. Awaisu yazo ya gaishe ta suka rakata har mota. Dreba na janta tunaninta yayi nisa. Kokonto take yi anya Gimbi bata yin wani abu domin takurawa Maamu? Sannan haka kawai take ji a ranta Bebi kanwarta ce ta kira Gimbi. To me ya hadasu. Da wannan tunanin ta isa gida. ***** Taxi ce ta ajiye Shuhada a bakin gate din gidansu maigadi ya taho da murnarsa ya tarbeta. "Hajiya hala babu wanda yasan kina hanya ba'a turo an dauko ki ba daga filin jirgi. Ina Suhailu dan makaranta?" Murmushi tayi tana janyo jakarta ya karba. Da ta shiga ciki tamkar ba gidansu ba. Duk wani abu da zai nuna sun taba rayuwa a ciki babu shi. Daga kan doguwar kujera ta hango Anti Bebi tana danna waya. Muryar maigadi yana tambayar Shuhada ina za'a kai mata akwatunan yasa ta dago kanta. "Da na ce kada ki taho gidan nan kinsan ba wasa nake yi ba ko. Zuwa yanzu yaci ace kinsan ni ba tsararki bace" Zama Shuhada tayi ta dora kafa daya kan daya "idan ban taho nan ba a titi zan kwana?" Anti Bebi ta mike tsaya tana kallonta. Yaushe ta fara sa'in'sa da ita. "Ki tattara ki koma inda gyatumarki take" "Itama gidan mahaifinta ta koma da kika kashe mata aure. Nima da kikayi nasarar kaso min nawa kinga sai nazo mu zauna a gidan nawa mahaifin." Da yatsa Anti Bebi ta nunata "ba'a ja dani Shuhada. Barin gidan nan shine kwanciyar hankalinki." Yatsan da take nunata ya kusa tsokale mata ido tasa hannu ta doke shi. "Kinyi kadan ki koreni daga nan. " Da yake ta juyawa kofa baya bata ji shigowar Alh Maitama ba babanta. Ita kuwa Anti Bebi ta riga ta ganshi sai kawai ta rike hannun da Shuhada ta doke ta soma ihu. "Kiyi hakuri don Allah kada ki sake dukana. Indai gidan nan ne yau zan barshi har abada" Tunani ta fara ko zautuwa Anti Bebi tayi sai taji tsawa daga bayanta. Kafin ta ankara har ya shigo yazo ya rungumeta yana mata sannu. Ita kuwa babu kunya ta cigaba da makale masa a gaban 'yarsa. Bakinciki fal zuciyar Shuhada ta juya zata bar wurin ya dakatar da ita. "Ba dole miji ya sakeki ba. Ina kallo kika kai mata duka sannan har na shigo ko gaisuwa babu zaki bar wurin" Hawaye take yi tace "Daddy kayi hakuri ina wuni" "Rike gaisuwarki bana so. Kuma ki sani indai zaki zauna a gidan nan ko kallon banza kika yiwa Bebi sai na saba miki." Anti Bebi ta langabe a jikinsa tana kallon Shuhada kasa-kasa. "Alhajina ka karbo albashin?" Jakar hannunsa ya mika mata yana murmushi "gashi amma na cire kudin mai gyaran mota da yayi min last week. Idan kin kasa kudin sai ki bani nawa ina son siyan wasu abubuwa" Shuhada kasa tafiya tayi don tsananin mamaki. Da gaske akwai mata marasa imani masu juya miji kamar waina. Ji Daddy dinsu mutumin da ake gani da mutumci da kima a waje ya dawo tamkar yaron goye a gaban mace. Kashewa Shuhada ido tayi sannan a hankali tace kadan kika gani. Da wannan bakincikin Shuhada ta ja kayanta hanyar tsohon dakinta. Anti Bebi ta tace cikin kissa "ki kai kayan dakina kafin nasa a gyara miki naki" Daddy ya juyo "Bebi kenan, kirkinki yasa kullum nake kara sonki." Shuhada ko waigowa batayi ba don kada ta ga karin kayan takaici. ***** Bayan tafiyar Mama da daddare Awaisu da Gimbi suna daki tana masa korafin jikinta na ciwo yace ta kwanta yayi mata tausa. "Shiyasa rannan Maamu take cewa da ma zan nema miki aikin da zaki tashi da wuri saboda ta kula ni da ke duk aiki yayi mana yawa." Tashi tayi daga kwanciyar "so take yi na dena aikin?" "Tace dai tana tausayinki ne. Tun farkon zuwanta ne muka yi hirar" "Uhmm humm" kawai tace bata kara magana ba. Zuciyarta tana kitsa mata nan gaba Maamu kokari zatayi ta fara juyasu. Wato har aikinta ya tsaya mata a rai. ****** Washegari Maamu ta tashi da gudawa. Tun dare Gimbi tace ayi miyar zogale. Awaisu yana wurin yace Maamu bata ci yana bata mata ciki. Sai Gimbi tace zata yi mata miyar kuka. To dama yanzu komai ta fada ya zauna sai ya amince zata yi din. Da ta tashi bata ce Laminde tayi mata wata miyar ba domin a ganinta barna ne akan 'yar miyar da ake zubawa Maamu kadan a sake kada wata. Haka aka kai mata tuwon da miyar zogale. Duk da tasan yadda yake yi mata amma dole ta ci saboda yunwa. Har su Rumana suka tafi Islamiyya karfe uku tana fama amma ta rasa wa zata fadawa saboda rashin Hausa. Shi kuma Awaisu tun asabar bai kara shiga dakinta ba. Laminde ta shiga kai mata abincin rana ta ganta tana bin bango saboda rashin kuzari zata shiga bandaki. Taimakawa tayi ta shigar da ita ta koma bakin kofa tana jira ta gama ta fito da ita sai ta fadawa masu gidan. Gimbi ce ta kirawota zata aiketa karbo dinki. Tana zuwa ta fada mata halin da taga Maamu. Gimbi tace to zata duba. Daga nan Laminde ta fita ita kuma ta manta. Shiryawa taje tayi tace Awaisu yazo ya kaita unguwa. Daya tambaye ta ina zata je tace gidan Anti Bebi. Shi dai yasan da bakinta take fadin halayen Antin wanda yasa basa hulda da ita. Amma ya kasa cewa komai sai mukulli da ya dauko. So take yi yau ta nunawa Anti Bebi yadda ta fara juyashi sannan idan da hali a dauke hankalin Mama daga sake yi mata tambaya akan Maamu. Bayan fitarsu Maamu tana kan toilet seat ta kasa tashi saboda gwiwarta duka babu kwari. A hankali cike da kasala ta rinka kiran Rumana da Laminde shiru babu amsa. Tun tana iya kiran har ta koma kuka. Tayi yunkurin tashi ta kasa sai taji kamar zata fadi. Haka ta koma ta zauna tana ta kiran mutanen gidan harda Gimbi. Bacci ne ya dauketa a wurin saboda gajiya da yunwa ga matsanancin ciwon kai. Harisu da Baaba Hure tayi mafarki wai sunzo daukarta. Ta farka a firgice. Rabonta dasu tun ranar da wayarta ta fada ruwa a bandakin. Kwan fitilar ya mutu tasa Rumana ta fadawa Gimbi har sau biyu ba'a gyara ba. Shine suke haskawa da wayarta. Tsautsayi yasa ta fadi har yanzu bata kunnuwa. Tun Maamu tana tunanin wani zai zo har ta hakura ta soma kokarin tashi. Tana mikewa ta zame a wurin ta fadi. [4:31PM, 2/18/2018] ‪+234 803 369 4017‬: *KASHE FITILA*💡16 *Batul Mamman*💖 Shuhada ta zuge wata 'yar madaidaiciyar jaka bayan ta gama hada kayan da zata bukata. Tun washegarin dawowarta ta yanke shawarar tafiya Kaduna wurin mamanta. Zama a gidan nan ko kadan bata jin zata tsinci wata riba. A kwana biyun da tayi babanta tamkar hoto haka take ganinsa. Bashi da wani motsin kansa sai abin da Anti Bebi tace. A wani firgice yake idan yana gabanta. Wannan abu ga rabowa da masoyinta Tajuddeen suka hadar mata suka karawa gidan zafi. Tana share hawaye yayar Tajuddeen ta kirata a waya. Tana dauka kuka suka saka a tare. Ko sati hudu Yayar batayi da dawowa Nigeria ba bayan ta raka mijinta conference Singapore. Kuma a gidan Shuhada suka zauna. Hakuri tayi ta bata sannan ta sanar da ita suna hanya ita da Gwaggonsu zasu zo bayar da hakuri har gida. Babansu ma yanzu zai bi Alh Maitama office ya bashi hakurin wannan cin fuska da aka yi musu. Shuhada cewa take yi babu komai ba sai sun zo ba amma suka dage. Tunaninta kada Anti Bebi ta wulakanta su. Zama tayi jefi jefi tana leka taga da ta ji karar mota. Tafi son ta fara hangosu idan sun iso taje ta tarosu. Tana cikin leken saboda jin an bude gate ta hango wata mota dark green ta shigo. ****** Kafin isowarsu Gimbi ta yiwa Anti Bebi text tana fada mata zasu shigo ta fito ta ganewa idonta yadda ta mayar da Awaisu. Dan mayafinta da ta saba ta dan rufe rabin kanta ta fito waje. Yana gyara parking Gimbi tace ya fita su gaisa da Anti Bebi. Kallonta yayi shiru yana nazari sai kuma ya fita din. Da sauri Anti Bebi ta karaso tazo gaban motar. "Oyoyo, oyoyo yau ga Awaisu a gidana" Dan rissinawa yayi zai gaisheta tayi saurin dafa kafadarsa. "Haba Awaisu dana. Ina kai ina durkusawa, sai kasa a kalleka ai" Hannunta da tasa a kafadarsa taki cirewa harda karkade masa wani dan zare daga wurin wuyansa. Wannan abu duk a idon Shuhada. Duk da bata kaunar Anti Bebi batayi zaton mugun halinta harda bin wasu mazan ba sai yanzu. Kuma tasan ko ta fadawa Daddy bazai yarda ba. Abu daya zatayi shine taje taci mutuncinsu daga shi har Anti Bebin ta huce haushi. Gimbi tana daga cikin mota murmushin fuskarta ya dauke ganin Anti Bebi ta dafa mata miji. Fitowa tayi ba arziki tace su shiga ciki. A nan suka bar Awaisu yana jiran fitowarta. Suna shiga Shuhada tana fara saukowa daga sama taji Anti Bebi tace "na manta uwar kishi ce kin wani bata rai don an taba miki miji. Dadin abin nima gidan aurena kika zo" Cikin tsiwa ta amsa mata "Anti kece sai wani dafa shi kike yi. Ni yanzu dai babu yadda za'ayi Maamu ta bar gidan lokaci guda? Kafin na samo kanshi wallahi duk dare yana dakinta ki rasa me suke yi. Wani lokacin sai na fara gyangyadi yake dawowa" "Gimbi anya baki fini tsiya ba. Wannan da nono na kika sha maza sun shiga uku mata sun ga ta kansu. Yanzu uwa da danta ma sai kin zargi wani abu. Ko don irinku Gimbiya da ina da da wallahi matarsa bata isa ta juya shi ba" Tafawa sukayi kamar sa'annin juna. "So nake yi ta koma garinsu kawai ya rinka yi mata aike. Zaman tare damu ne bana so. Duk abi a sawa mutane ido. " Sai ta dan rage murya har sai da Shuhada ta dan kara bene biyu domin taji da kyau. Dayake wurin zagaye ne basa ganin juna "Kuma ina so ko za'a dauke hankalin Mama daga kan gidana. Ai na fada miki ranar da tazo yadda muka kare" Anti Bebi ta hangame baki " Iyye, Gimbiya kina burgeni. Kin cika mace wadda tasan meye 'yancin rayuwa. Wasu 'yan bokon miji da danginsa suyi ta gasa su amma sai su rinka iyayi wai basa bin malamai. Kuma duk karya ne. Tunda da kanki kika nema to kisawa ranki Amina ta bar shiga sabgar da baki sakata ba" Duk da Gimbi bata so abin ya kai haka ba amma ta fara jindadin mallaka da juya miji. Burinta karuwa yake yi domin yanzu har ogansu a banki take son ya dena mata maganar latti. Shuhada tana tsaye zuciyarta har bugawa takeyi don tsoron matan nan. Wannan wace irin masifa ce muke daukarwa kanmu akan duniyar da bazata dore ba. Komawa tayi saman a hankali jikinta a sabule. Sai a lokacin taji tausayin mutumin da hannun Anti Bebi ya taba. Lallai ya aurowa kansa masifa. ***** Karfe biyar da rabi Laminde ta dawo gida. Tasan dama yaran suna Islamiyya. Rashin ganin Gimbi yasa tayi tunanin ko sun kai Maamu asibiti, kwarai taji tausayinta dazu. Ku6ewa ta zauna gurzawa kafin su dawo a bata shinkafar tuwo ta dora. Tana aikin su Rumana suka shigo. Dakinsu ta wuce ta cire kayan makaranta sannan ta shiga bandaki yin alwala saboda an fara kiran magariba. Tana budewa ta ga Maamu a kwance ko motsin kirki bata yi. Ga jikinta alamun ta sake yin gudawa a wurin. Ihun kuka Rumana ta saka tana kiran Laminde. Sai gata a guje tare da su Haris. Duk su biyun sun rude suna zaton ta mutu ne. Suna kokarin dagata su Awaisu suka dawo ya tsaya wurin maigadi Gimbi ta shigo. Daula ce ta fada mata Maamu babu lafiya tabi bayanta. Daga bakin kofar bandakin ta toshe hancinta. "Hmmmm warin meye wannan haka" Tana kallo da kyar Maamu take bude ido ta jingina da jikin Rumana ita kuma Laminde tana tara ruwa a bokiti da zata dauraye mata jiki tace . "Maamu ce babu lafiya, a kwance nan muka ganta" Tabe baki tayi "Toh, to Allah Ya sauwake. Gyara mata jikin kafin na dawo" Tana fita ta ga Awaisu a falo Haris yana fada masa. Da sauri ta karaso da alamun gigicewa har tana jifa da mayafi. "Abban Haris juya mu kai Maamu asibiti bata da lafiya." Duk yadda yake nuna rashin kulawarsa damuwa ce ta ziyarce shi ya ruga dakin a guje. Ganin Rumana ta kasa rike Maamu sosai kafin Laminde ta dauko musu nata sabulun saboda nasu saura guntu da suke amfani dashi anki basu wani. Mantawa yayi da kayan jikinsa ya shiga ciki ya dagata ya saka a bahu sannan ya soma dibar ruwan yana wanke mata jiki da hannunsa yana kiran sunanta cikin tashin hankali kada ta mutu. Da Laminde ta kawo sabulun hannun Rumana ta ja suka fita ta rufe kofar. Rumana tana son komawa Laminde ta girgiza kai. "Ki bar Kawunki ya sami ladan mahaifiyarsa Rumana. Dauko mata kaya kafin ya gama" "Namiji ne fa" ta fada tana yatsina fuska. Tuni Kawun nata ya fice mata a rai. Laminde tayi murmushi "to naji bari naje ya bani nayi mata wanka" Gimbi ce ta shigo tana tambayar yana ina suka nuna mata bandakin. Muryarsa taji yana cewa "Gimbi zo kiyi mata wanka zan chanja kaya muje asibiti" Gabanta har faduwa yayi, wannan kazantar ta jikinta zata taba..... Laminde tana kallonta sai ta shiga tace zata yi mata. Tsoro taji kada da gangan Gimbi ta saketa ta fadi. Bayan anyi mata wankan ne Laminde ta kula hannunta daya ya kumbura ta wurin babban yatsanta ga dukkan alamu tayi targade. Haka ta shiryata Awaisu da Gimbi suka kaita asibiti. Suna can ya kasa zama har likita ya fito yace suna mata karin ruwa sannan anyi mata gyaran targade. Hankalinsa duk baya jikinsa sai da ya ganta. Da kyar take magana idanu duk sun fada ciki tace ya kirawo mata Harisu a waya. Gimbi jin an ambaci sunan daya makiyin nata ta kasa kunne sai dai bata jin me Awaisu yake fada da yarensu har ya gama wayar. Juyowa yayi yace "Gobe in sha Allah Yaya Harisu zai zo da daya daga cikin matansa da Baaba Hure. Ina tsammani zasu taho da kanin Maamu ma. Ki kira Laminde a gyara musu dakin baki kafin mu koma gida" Kirjinta ne ya buga, mutanen da ta raina zasu cika mata gida. [4:31PM, 2/18/2018] ‪+234 803 369 4017‬: *KASHE FITILA*💡17 *Batul Mamman*💖 Awaisu bai lura da yadda Gimbi ta chanja da wuri ba daga jin maganar zuwan su Harisu ya mika mata mukullin mota. "Kije gida ki taho muku da kayan bukata na kwana. Idan kin dawo sai na tafi da motar" Zaro idanu tayi tana neman amsar da zata bashi domin gujewa kwana da Maamu. Itama Maamu da ta gane me ya fada murya can kasa saboda ciwo tace masa ya tafi da matarsa a kawo mata Laminde ko Rumana. Da ta ga zaiyi gardama tace saboda yara ne. A ranta kuwa cewa take gara ta kwana ita kadai da a barta da Gimbi. ***** Harisu dakin Baaba yaje ya fada mata Maamu babu lafiya. Hankalinta kuwa ya tashi tace to yaje ya sanarwa 'yan uwanta. Har zai fita ta sake kiransa. "Dangin mahaifin Awaisu ma ya kamata ka fada musu. Ai kana jin yadda suke yada mana magana wai ya tare a jikinmu baya musu komai" Harisu ya sha kunu "haba Baaba har yaushe zaki bari zancensu ya dameki. Allah Yana gani yadda duk zuwansa garin nan sai yaje kuma yayi musu alheri. Neman rigima ne kawai" "Duk da haka kaje ka fada musu ko zasu tura wani yaje dubiya". "Har na fadawa Awaisun kila muje da kanin Maamu ko wani dai cikinsu. Mu da zamu je dubiya kada kuma a dorawa iyalinsa wahala" Baaba Hure tayi wani murmushi wanda ita kadai ta san ma'anarsa. "Baka saba yi min musu ba Harisu. Nace ka fada musu yadda zasu tura wakilinsu dubiya. 'Yan uwanka ma zan sa a kirasu a waya ko mutum biyu a samu. Cikin matanka ka dauki babar Rumana saboda ta gano 'yarta tunda ka hana a kawota hutu. Sauran suma a hankali sai kaje dasu tare ko daya bayan daya" Harisu kasa motsawa yayi jin wannan hadi na Baaba. Duk girman gidan Awaisu idan sukayi yawa zasu takura musu ne. Ga mara lafiya kuma ga baki da wanne zasu ji. "Yaya kaki tafiya ne?" Takalmansa ya saka yayi waje. Ita kuwa Baaba Hure ta gyara kwanciyarta tana jira ya dawo ya kira mata Awaisu ta ji yaya jikin Maamu. Ba komai yasa take son tarawa Gimbi jama'a ba sai bakar maganar da suka yi mata ita da Anti Bebi a rashin sanin bahaushiya ce. So take ta tabbatar Gimbi bata son dangin Awaisu da gaske ne ko kuwa dai 'yar tsama ce irin ta mata da dangin mijinta. ***** Gidansu Maamu ya fara zuwa inda duka yayyenta maza da kanne suke tare da iyalansu. Bangaren wani cikin 'yan uwan yaje suka gaisa ya sanar dasu abin da ke faruwa. Nan da nan 'yan uwa suka taru ana jajantawa sannan suka ce zasuyi shawara wanda zaije a madadinsu. Harisu yana fita Hajja Jume matar babban wan Maamu wanda ya dade da rasuwa ta dogaro sandarta ta taho. "Yanzu labari yazo min za'a tafi wurin Safara'u dubiya ko" Bashar wanda yake matsayin babba yanzu ya hade rai yana hararar Atika jikar Hajja uwar hada gurmi. "Tikeke akan gulma zanyi maganinki" Hajja ta daga sanda tana fada "wanda ya fasa Bashar, nace wanda ya fasa. Yarinya duk kun takura mata kamar ita kadai ce jika. Duk abinku a nan gidan zata zauna. Bani da kowa a gabana sai ita. Tunda tazo ku da iyalanku kun hade mata kai kamar ka jininku ba" Tikeke ta sunkuyar da kai ita a dole a bar tausayi ce "Hajja babu komai dama na fada miki ne kada a gama rabon waye zaije Abuja gidan Kawu Awaisu a barmu a nan" Hadi yayi caraf yace "kada ma kusa rai, ni da Yaya Bashar zamu je. Ai ba gayya za'ayi musu ba" "Wallahi baku isa ba Hadi. Ni zaku nunawa wariya don nawa mijin ya rasu. To ni da Tikeke kamar munje mun gama. Idan da kara ni ya kamata na fadi masu zuwa tunda yaron nan dana ne. Malam da Safa'ra'u ciki daya suka fito ba kamar wasu 'yan uba ba" Hayaniya ce ta kaure sosai a tsakaninsu karshe aka tsaya akan za'a tafi da Tikeke, Kawu Bashar da matar Hadi. Idan basuyi haka ba tijarar Hajja bata tsallake kowa. Ba karamin aikinta bane ma tasa danta baban Tikeke ya kaisu tunda dreba ne. **** Kasuwa Harisu ya koma can wurin masu gwanjo ya hadu da Bomai kanin baban Awaisu. Dattijo ne rigimamme na ajin karshe. Yana cikin masu yiwa Harisu habaici wai sun shanye Awaisu baya bi ta kansu. Bayan jarin gwanjon ma shine ya bashi. "Alh Harisu kenan, yau an leko mu" "Kawu Bomai yaya kasuwa?" Kan benci ya zauna yana zukar sigari kafa daya kan daya. "Gata nan muna fama. Yaya akayi ne?" Kamar yadda ya sanar da 'yan uwan Maamu haka ya fadawa Bomai. Wani tsalle ya daka ya tashi dama shi ba jiki ba sai tsawo. "Maamu tamu ce babu lafiya? Kace ban ga ta zama ba. Kayi kyan kai sosai da ka fada min. Asubar fari zanzo nan gidan naka mu tafi" "Sai wuraren karfe tara zamu tafi. Nace su sauran zaka sanar dasu ko naje na fada musu. Awaisu yace jikin da sauki dai" Matsowa yayi daf da Harisu "Tunda na sani ka bar maganar kawai ni zan sanar dasu." Sai kuma ya gyara tsayuwa yana kwantar da kai gaban Harisu "Maamu mutun ce, wato ba don haduwarta da Mal Sa'adu mai rasuwa ba dama ni naso na aureta saboda kula da maraya. Kuma gashi ni ban haihu ba. Shiyasa nake jin yaron nan a raina sosai. Kaga sau biyar fa yana bani jari. Yaro yayi halin iyayensa wurin karamci" Harisu gyada kai kawai yake yi ya samu ya bar wurin. Baaba Hure ta hadashi da aiki. Me zai sa tace kowa sai yaje. Tausayin Awaisu da Gimbi wadda za'a hada da baki ne ya kama shi. Yana kallo Bomai ya kulle gwanjonsa ya saba a kafada yayi hanyar titi. ***** "Hinde maza maza fito ki fara hada kaya" Hinde na bandaki ta fito da sauri bota a hannu. Ajiye botar tayi ta sa hannu ta toshe gefen hanci ta rangada guda tana tafa hannuwa "Ayyiriririiiii, sai yau kaga damar sakin nawa, to ka sani kuma ka jira ina gama idda zan sami miji da ya amsa sunansa ba irinka ba kashi da rai. Nawa kayi min ne sakin" Botar da ta fito da ita ya dauka ya kafa a baki ya sha ruwan sannan ya kuskure baki ya tofar. "Dadina dake wutar ciki, baki ji bayani ba kin hau suki burutsu. To ai sai ki tafi nima na huta" "To dai gaya min me ya faru idan ba sakin bane kake min wannan kiran" Kan kullin gwanjon ya dare ya zauna "Abuja zamu koma gidan dana" Wata muguwar shaka Hinde tayi masa har yana zaro idanu "munafuki ashe har da gareka ban sani ba. A wace tashar ka hadu da babarsa" Hannunta yake duka da kyar yana cewa "Awai,aaaaw,awsu" Sassauta rikon tayi yace "AWAISU ne fa dan marigayi yayana. Kasheni zakiyi ne?" Hinde ta zauna shirim a gefensa tare da murza masa wuyan. "Kaine baka iya kawo labari ba. Kace Awaisu na Maamu" Nan ya labarta mata yadda sukayi da Harisu da kuma kudurinsa "Yace kwana biyu zamuyi. Amma so nake ki hada kayan kamar na sati. Sai kuma mu saka kamar uku uku a jikinmu kada a ga Ghana mazigo din kayanmu da girma. Idan munje zan sa ya nema min aiki. Kema ki rinka yiwa Gimbiyar nan ladabi. Kinsan durkusawa wada ba gajiyawa bane." Hinde sai murna zasu Abuja. Ko Bomai bai fada ba bata ga dalilin da zaisa idan sun je ta dawo Fika ba. Kallonta yayi ta shige daki ta fara fiddo kayansu zata wanke yace "Hinde don Allah idan munje kada ki nuna hali, banda dauke dauke kinji ko" Harara ta galla masa idonta kamar ya fado. Me zai kaita sata kuma yanzu, ita da tayi a gidan biki 'yan mata sukayi mata duka sai da hakorinta na kasa ya cire. ****** Daren ranar Gimbi kasa bacci tayi. A haka ma don bata san mutum nawa ne masu zuwa ba. Sau biyu Awaisu yana farkawa ya ganta a zaune sai tace masa jikin Maamu ke damunta. Gashi likita yace harda rashin cin abinci sosai. Harda kukanta tace "My dear ko zaka tambayi Maamu me tafi so sai na rinka dafa mata. Gobe zan dauki hutu ko na sati ne na kula da ita" "Kema kinsan bazasu baki wannan hutun ba. Ki bari kawai tunda akwai masu zuwa" Murmushi tayi, don tana tunanin a goben Anti Bebi zata kaiwa Wangesi bukatarta akan ogansu. Sake marairaicewa tayi "Duk laifina ne da nake zuwa aiki bana iya kulawa da ita yadda ya kamata. Kullum da safe idan naje fada mata zan fita Maamu sai tayi min addua. Yanzu idan suka zo aka ce na barta da yunwa fa." Kuka ta fashe dashi Awaisu ya rarrasheta. Karshe tace masa zata bar aikin kawai ta kula da gida. Ga mamakinta sai taga ya bata goyon baya. A zuci tace wato shima bakinciki yake da aikin. To yanzu ta fara. ***** Da safe tunda babu Laminde gashi tana son burge Awaisu haka tayi farfesun kayan ciki da dankali ta hadawa Maamu Awaisu ya kai asibiti. Bayan su Haris sun tafi makaranta ta fadawa Anti Bebi halin da take ciki da bakin da zasu zo. "Zage damtse zakiyi ki kyautata musu kada wani ya sami bakin magana akanki" inji Anti Bebi. Ai kuwa ta wuni a kitchen tana girkin tarbar baki mutum hudu ko dubiya bata samu zuwa ba. Sai yamma likis suka iso mota biyu. Awaisu ma shigowarsa kenan kuma Haris yayi masa waya ya sanar dashi karin da aka samu yace ya amince duka su taho tare akwai wurin kwana. Sai dai kuma ya manta bai fadawa Gimbi ba. Jin tsayuwar mota tabi yaranta suka taho da gudu tarbarsu Baaba Hure. Sai ga Gimbi murmushi ya makale a gefen baki. Mutane ta gani wanda ta sani da wanda bata taba gani ba. Baaba Hure, Anti Ummukulsum, Harisu, Maman Rumana, Kawu Bashar, Ammu matar Hadi, Tikeken Hajja, Bomai da matarsa Hinde. Mutum takwas. Tun a zuci ta fara kuka. [4:31PM, 2/18/2018] ‪+234 803 369 4017‬: *KASHE FITILA*💡18 *Batul Mamman*💖 Zuciyar Gimbi harbawa ta rinka yi sosai saboda wani bacin rai da ya danneta. Kasa daurewa tayi duk iya kokarinta ta fashe musu da kukan bakinciki mai sauti. Ai kuwa hankalinsu Baaba Hure ya tashi matuka sun zata ko Maamu rai yayi halinsa ne. Da yake ta fara kwarewa da kissa irin ta Anti Bebi sai tayi saurin goge hawayen harda rungumo Baaba tana kallon Harisu a zatonta shi kadai yake jin Hausa. "Wallahi tsabar murnar ganinku ne Yaya. Tun jiya da yace zaku zo nake murna. Allah Sarki Maamu yau zan gani ni da ita wa yafi murnar zuwanku" Daga gefe taji ance "kissa adon mata, Bomoi ka ga wadda ta fini" Hinde ta fada da sunan rada duk da tasan ana jinta kuma da hausa. Bomoi ya galla mata harara ya kalli Gimbi yana murmushin dole. Daga zuwansu zata nemi janyo musu bakin jini wurin matar gida. A razane Gimbi ta kalli Hinde har cikinta yana kadawa. Sakin fuska tayi ba arziki kamar bata fahimceta ba tace su shigo ciki. Mukullin wani daki ta waje ta bawa Harisu inda ya taba masauki lokacin zuwansu Hajji. Nan suka shiga shi da Kawu Bashar da Bomoi wanda yake ta zuba surutun haduwar gidan dansa gudan jininsa. Daula ce tayiwa Baaba Hure jagora zuwa dakin Maamu inda zata zauna. Wani daki a gefensa kuma Gimbi tace Ummukulsum, Maman Rumana, Ammu, Hinde da Tikeke su shiga suyi wanka sannan su fito cin abinci. Tikeke ta zumburo baki "Haba Hajiya ko ruwa bamu sha ba zaki ce muyi wanka. Allah Ya gani sai naci abinci nake iya komai." Ammu ta riko hannun Tikeke tana kokarin fita daga dakin zata koma falo inda ta hango kwanukan abinci an jere su. Kokawar fizgewa Tikeke ta somayi Ammu ta canja harshe tace zata fadawa Kawu Bashar. Rai a bace ta kwace hannunta ta shiga bandakin tare ta bugu kofa. Jiki a sanyaye Gimbi ta fita daga dakin. Yau kuma irin bakin da tayi kenan ta fada a zuci. Falon taji kamar yana warin gumi a cewarta ta dauko air freshner ta shiga fesawa. Juyawar da zatayi ta hada ido da Baaba Hure tayi saurin ja da baya. Baaba ta saki fuska "Dama kwan fitilar bandakin ne naga ya mutu. Idan akwai wani ki taimaka a saka min don in yamma tayi ba gani nake sosai ba bare kuma a duhu" Mamaki ne ya bayyana sosai a fuskar Gimbi jin Baaba tana hausa. Dazu ma taji wata tayi a waje. Yanzu bata isa ta juya harshe tayi gulmarsu a gabansu ba kenan. "Baaba bari idan Abban Haris ya dawo sai a saka miki ki shiga" Baaba ta dafata da hannu daya tana dan tafiya "muje ki kaini naki sai nayi alwala a can. Banyi sallar la'asar ba ga magariba tana gabatowa" Ba'a son ranta ta kai Baaba bandakinta ba. Maamu kuwa ko hanyar dakin bata taba takawa da kafarta ba. Tana zaune tana ji Baaba Hure tana kaki. Takaici ya isheta ta fita ta koma dakin Awaisu sannan ta kira Anti Bebi. "Na shiga uku Anti, su takwas kamar ance musu ta mutu. Ina zan kaisu" "Ba na son shirme kinji ko. Ki tashi ki je duk yadda suke so kiyi musu. Idan kika bari suka gane wani abu to karshenta su ki tafiya da wuri. Kinga garin neman gira kin rasa ido" Maganar Anti Bebi gaskiya ce. Da saurinta ta shiga kitchen ta dora macaroni tunda dama shinkafa da miya tayi da kuma tuwon dare. Kafin ta gama Awaisu ya shigo ya tafi wurinsu Harisu suna gaisawa. Sai da sukayi sallar magariba suka ci abinci sannan suka fara shirin tafiya asibiti gabadayansu. Gimbi tana ta raha da rawar kai ita me son surukai. Sun firfito waje Awaisu ya kira drebansa da yake kai yara makaranta ya bashi mukullin mota "Sunday gashi ka debe su Yaya Ummukulsum ka wuce dasu asibitin da aka kwantar da Maamu. Zan tsaya a atm ne sannan na taho da su Baaba" Sunday ya dan rissina a ladabce "Oga yaushene Hajiya babu lafiya, wane asibiti ne.?" Awaisu yaji kamar ya raina masa hankali yace "Inda ka kai musu abincin rana mana" "Ban fita ba tunda mun dawo da su Haris" Idanun Awaisu suka kankance yana kallon Gimbi "da kanki kika kai musu abincin rana? Ina na daren ne ma ban ga an dauko ba" Idanun Gimbi nan da nan suka yo waje ta rasa amsar bayarwa. Baaba Hure tana kallonta tasan bata da gaskiya "Gimbiya kada kice min ba'a kaiwa Maamu abincin rana ba bare na dare" "Uhmmm, uhmmm" nan fa jikinta ya soma rawa ganin idanu a kanta ga Awaisu yana wani huci kamar mayunwacin zaki. Irin wannan fushin nasa ba kasafai yake ba. Kuma a tunaninta yanzu da Wangesi ya gama masa aiki bai isa yayi mata ko da mugun kallo ba. Tsawa ya daka mata kamar ya kai mata duka "ki bani amsa mana" Harisu ne yayi magana ganin ransa da na Baaba Hure a bace yake. Yaran ya fara cewa su shiga motar Sunday sannan yace "Awaisu meye haka ne kake yi mata tsawa gaban yara. Gimbiya an kai abincin?" Kuka ta saka saboda tsabar bata damu da Maamu ba shaf ta manta da batun abincin. Na safe ma da tayi saboda ta burge mijinta ne yaji dadi. "Wallahi Yaya Harisu ina ta aiki ne na sha'afa." Ummukulsum tace "wannan ba magana bace Gimbi. Akwai wani aiki da zai sha kanki sama da nata da take asibiti? Yanzu ga jinya ga yunwa daga ita har Rumana" Ido sharbe da hawaye ta rinka basu hakuri. A ranta kuwa duk tsine musu take yi suna neman jaza mata masifa wurin miji. Baaba Hure tamkar ta cinyeta da fada. Tana yi Awaisu yana yi don ya kule karshe. Harisu ne ya rinka basu hakuri. Su Tikeke kuwa an sami abin kallo da gulma. Marasa jin hausa sosai babu damar tofawa. Duk wani haushin Gimbi da yake ji kwanakin baya ya kasa magana tun jiya da ya ga Maamu a wannan yanayin yaji kamar an bude masa ido. A fusace yace mata taje ta dauko abincin. Wani tsoron ya sake kamata domin batayi dasu ba. Hasali ma dai babu sauran abinci a gidan. Awaisu yayi fadan da hausa ya koma saka yarensa kamar ya kai mata duka. Baaba Hure ko a jikinta saboda tun maganar da sukayi akanta take jin Gimbi ba matar kirki bace. Harisu ya ja shi gefe ya soma nasa fadan "Wani sabon salo ne ka koya zaka zubarwa matarka mutumci a gaban baki. Dubi yadda suke kallonka. Kana tunanin wannan labarin bazai je Fika ba" Kwalla ce take barazanar fita daga idonsa saboda tunanin yaya Maamu ta wuni. Yaje da azahar daga wurin aiki amma ita dasu Laminde babu wanda ya fada masa "Yaya ace tun abincin safe saboda Allah" Harisu ya dafa shi yana murmushi "to kuka zaka yi min? Awaisu 'ya'yanka hudu fa. Muje su koma suyi girkin kafin dare ya karayi a hanamu shiga" "Bari kawai ma saya a hanya. Karfe tara suke hana shiga sai goma na safe kuma" Tare suka koma suka shiga motocin. Wasu na motar Sunday tunda babba ce school bus sauran Awaisu ya diba. Gimbi tayi turus a waje ganin Bomoi ya shige gaba abinsa. A dakile Awaisu ya nuna mata bus din "Idan zaki je ki koma bus din inda mata suke" Ranta na kuna kamar tace bazata ba ta koma ta shiga tsakiyar Ammu da Hinde. Kallonta suka rinka yi ta kasa motsin kirki saboda sun matseta. ***** Suna zuwa a kwance suka sami Rumana a gadon da yake gefen na Maamu tana bacci. A kasa kan abin sallah kuma Laminde ce take cin dafaffiyar gyada. Naira hamsin gareta shine ta siyo musu ita da Rumana suka ci suka sha ruwa. Maamu taki ci tana kwance tana hawaye. Yaushe ne danta zai waiwayeta??? Muryar Baaba Hure taji ta soma yunkurin tashi. Maman Rumana ke rike da hannunta ta karasa da ita bakin gadon saboda dishi dishi take gani. A haka ma don anyiwa idon aiki ne. Hannu ta mika tana laluben Maamu. Ji tayi Maamu cikin muryar dake nuni da tana jin jiki tace "Baaba" Baaba Hure sai hawaye "Maamu sannu, sannu 'yar uwa. Kai Awaisu ku zuba mata abincin nan" Gimbi ce tayi saurin mika hannu zata karbi ledojin ya harareta sannan ya bawa Maman Rumana. Ummukulsum tace "Maamu kin rame sosai" Riko hannun Ummukulsum din tayi "hmmm kayya Ummu jikin tsufa ne kawai, Ina yaran , yaya wajensu Auta Zakiyya" Rumana cikin bacci taji kamar muryar babanta. Firgigit ta tashi. Abin mamaki harda Mamanta da Baaba. Wani tsalle tayi ta diro ta kankame Harisu. Shi kam kunya ma ta bashi a gaban mutane. Ta tafi zata rungume mamanta ta harareta irin abin 'yar fari. Sai kawai ta koma jikin Baaba ta kankameta. Sun gama gaisawa Laminde da Rumana suna gefe suna cin abinci sauran suna ta hira. Basu bar asibitin ba sai shadayan dare. Nurses suna ta zuwa ana cewa su bar hayaniya. Likita ya bukaci ganin Awaisu kafin su tafi. Fada sosai yayi masa duk da karancin shekarunsa akan shi na barin Maamu da yunwa. Duka allurai da maganinta tun azahar ba'a yi mata ba saboda bata ci abinci ba. Sannan jikinta ma yana nuni da alamun rashin kuzari saboda tana bukatar wasu sinadarai a jikinta. Shi dai sai hakuri yake bayarwa yana tunanin wai me Gimbi take yi har Maamu take zama da yunwa. A wani bangaren tuhumar kansa yake da rashin kulawa wadda bai san dalilinta ba ****** Wurin shabiyu da rabi kowa yaje ya kwanata Awaisu da Gimbi suna ta fada. Bashi hakuri take yi amma kamar tana ingiza shi. Bandaki ta shiga tayiwa Anti Bebi text ta sanar da ita. Shawara ta duk da batayi mata dadi ba haka ta karba kafin gobe ta nemi Wangesi. Wurin Baaba taje tayi sa'a bata kwanta ba. Nan ta kwantar da kai ta bata hakuri ta roketa akan ta bawa Awaisu hakuri. A zatonta tuban gaskene tacewa Awaisu magana ta kare daga lokacin. Ya dai ce to amma juya mata baya ma yayi da suka kwanta. Kafin nan kuma yasa ta bawa Ammu da Maman Rumana dakinta saboda wancan yayi musu kadan. Ita Ummukulsum ta canji Laminde zata kwana a asibitin Da safe matan suka tayata girki tana ta kokarin jansu a jiki. ***** Anti Bebi karfe bakwai ta fice daga gida sai kauyen Nasarawa state inda Wangesi yake. Magunguna ya bayar da wasu layu da za'a binne a gidan. Kafin shabiyu ta dawo gida. Wanka tayi ta shirya sannan tace Alhaji yazo ya kaita dubiyar surukar Gimbi. Tun tana chan zazzabi ya kamashi a office ya dawo gida. Wani nau'in asirin akayi masa. Da ya dawo Shuhada ce ta tarbe shi ko kallonta yaki yi. Kudin mota take so ya bata itama ta bar musu gidan. Suna fitowa daga daki Anti Bebi ta marairace wai yace Shuhada tazo suje tare saboda zaman gidan bazai mata dadi ba. Har ransa yaji dadin ta damu da yarsa amma ita Shuhada bata sonta. Dolenta ta fito suka tafi tare. Anti Bebi ta hakimce a baya Shuhada na gaba. Daga bayan mota take ta bashi umarni yana toh kamar wani bawanta. Kafin su je asibitin Shuhada har kuka tayi ganin yadda Daddynta ya koma a gaban mace. ***** Alh Mudi da Mama suna bayan mota dreba na jansu zasu je duba Maamu. Fada sosai yayiwa Gimbi a waya bayan ya sami labarin rashin lafiyar a bakin Saminu. Su da suke garin ace basu da labari har su Harisu sun zo shi kuma Saminu yana hanya. Gimbi hakuri ta bayar kawai. Yadda bata damu da Maamu ba bata ga dalilin da sai sunzo dubiya ba. Dakin yau a cike idan kaga Maamu da Rumana tamkar ranar sallah. Su Mama ne suka fara zuwa ana gaisawa sai ga Anti Bebi ta shigo tana fara'a. Tuni Gimbi ta rikice ganin kallon da Mama da Alhaji suke yi mata. Ita kuwa Anti Bebi don ta bawa Mama haushi ta tafi ta rungumo Gimbi "Gimbiya yaya mai jikin. Tun shekaranjiya da kika fada min hankalina ya tashi. Jiya da kika min waya kuma baki ne dani ban samu nazo ba" Mama ji tayi kamar ta rufe Gimbi da duka a wurin. *KASHE FITILA*💡19 *Batul Mamman*💖 Kallon kallo aka rinka yi tsakanin Gimbi da iyayenta. Gashi maganganun Anti Bebi sun sa ta daskare a wurin kamar wata dutse. Anti Bebi tana lura dasu ta share tana dariya ita kadai a zuci. Wato don rainin wayo irin na Gimbi so tayi ta rinka morarta a bayan fage batare da ansan tana kula ta ba. In dai Anti Bebi ce bata isa ba. A ganinta duk abin da take yi neman 'yanci ne. Saboda haka idan zaka sha giya gara kasha ta dubu. Alh Mudi ba a son ransa ya gaisa da Alh Maitama ba. Shi fa komai da ya danganci Anti Bebi to baya baya dai. Lokacin da take auren wani dan unguwarsu tamkar zautacce ya koma. Duk inda ya zauna sunanta yake kira kuma ko a baya idonta baya taba saba umarninta. Mama ta daure ta cigaba da hira da mutanen dakin tana tambayarsu yaya maijiki. Lokaci lokaci take kallon Gimbi wadda har yanzu bata farfado daga mutuwar tsayen da tayi ba. Harisu da Alh Mudi da sauran mazan suka fita suna hira. Sai dai Alhaji hankalinsa baya wurin sosai. Karshe ma dai yace musu zasu tafi saboda yamma tayi sai gobe zasu dawo. Wayar Mama ya kira ita kuma a lokacin tana ganin Laminde ta hada kwanukan abinci zata kai mota tayi saurin bin bayanta. "Laminde dan tsaya don Allah" Laminde ta tsaya har Mama ta karaso ta sake gaisheta tana dan murmushi. Fuskar Mama ta kalla mai nuni da damuwa. Mama tace "matar nan da ta shigo da mijinta kin taba ganinta a gidanku?" "Anti Bebi ko? Inace kanwarki ce inji Hajiya" Mama ta rike baki, lallai akwai abin da Gimbi take yi wanda basu sani ba. "Tun yaushe kika fara ganinta a gidan?" Dan tunani tayi sannan tace "gabanin zuwa Maamu ne" Kuka ne kawai Mama batayi ba don takaici. A take zuciyarta take raya mata Gimbi ta fara bin sahun Anti Bebi. Hannun Laminde ta rike kana ganinta kasan cikin damuwa take sosai "ki taimakeni Laminde duk ranar da ta sake zuwa ki sanar dani. Kuma ni na baki dama kisa ido sosai akan uwar dakinki. Idan kinga wani abu da kike ganin tayi bai dace ba kada ki boyemin" "To Mama in sha Allahu." Mama godiya tayi mata sannan ta wuce. Laminde har tausayinta taji. Iyayen Gimbi mutanen kirki amma ta rasa inda ta koyo wannan halin na cutar da uwar mijinta. ***** A cikin dakin Anti Bebi ta sake tana ta yiwa bakin Gimbi hira tamkar sun dade tare. Alh Maitama yana tsaye shi kadai namiji cikin mata. Murmushi tayi don tasan izininta yake nema tace ya fita gasu nan zuwa. Kamar an tsikare shi ya fice. Shuhada ta sunkuyar da kai don kunya sai ga hawaye. Wannan tozarci har ina. Dole ma ta bar gidan kafin bakinciki ya kasheta. Da tunanin Tajuddeen zata ji wanda yayi mata sakin wulakanci duk kuwa da son da suke yiwa juna ko yadda mahaifinta ya koma. Baaba Hure ce ta kula da hawayen da Shuhada take gogewa tace " 'yan mata me ya sameki?" Anti Bebi tayi caraf ta tashi harda rungumota a jikinta. "Sharrin namiji, cikin dare mijinta ya dawo haka kawai ya dankara mata saki uku ba laifin zaune babu na tsaye. Ko sati uku ba'ayi ba. Idda ma take yi. Shuhadana ki rinka hakuri. Shiyasa fa nace ki fito kisha iska kada tunanin namiji ya sa miki hawan jini" Tamkar Shuhada ta shige kasa don kunya. Yanzu me ya kawo fadawa mutanen da bata taba gani ba sirrinta. Tunawa tayi babu wanda yasan lokaci da yadda sakin ya faru sai Suhail shiyasa ta kalli Anti Bebi a razane. Wannan shegen murmushin ta sakar mata mai nuni da tasan komai. Tsanarta ta sake samun wurin zama a zuciyarta. Gimbi ta kasa zaune ta kasa tsaye tun bayan fitar Mama. Ita a tunaninta ma ko kiranta zatayi a waya aci mata mutumci. Shirun da taji yasa hankalinta ya dan kwanta. Fita tayi daga dakin zata leka ko sun tafi Anti Bebi tayi sallama dasu Maamu tabi bayanta. Dan nesa da motar Alh Maitama suka tsaya Gimbi ta juyo a tsiwace "Anti Bebi ya zaki min haka? Meye na zuwa asibitin gashi yanzu Allah kadai Yasan me su Baba zasuyi min" Gira ta daga tana yatsina fuska "sannu uwar munafukai, da cewa akayi dake ni bani da hankali. Kin iya kawo mijinki na kaishi a baki akalarsa a tafin hannunki amma bazaki nunawa duniya matsayina na kawar babarki ba. Haba Gimbiya, dube ni da kyau nafi karfin wani shege yabi ta kaina ya gina kansa sannan yasa kafa ya tureni." Gimbi ta fusata "nice shegiyar?" "Yo nufinki nice? Kada ki kuskura kice zaki min rashin kunya Gimbiya, sai nasa ki raina kanki. Bar ganin na hadaki da Wangesi ba dashi kadai na dogara ba. Awaisun da kike takama dashi sai nasa a mayar min dashi tamkar wancan Alhajin. Idan naso albashinsa ma ni zai rinka bawa ajiya" Gimbi taji cikinta na karar tsoro amma tace "mu zuba mu gani, sai na tona miki asiri" "Bani da sirrin boyewa, ke dai matsoraciyar banza ki jira hukuncin iyayenki a kanki. Kuma kisa a ranki tamkar na rama wannan rashin mutumcin naki na gama. Bebi ce fa, Bebin maza mata su ganni su watse" Duk da Gimbi tana tsoron Anti Bebi dakewa kawai take taja tsaki ta juya. Ido hudu sukayi da Shuhada wadda ta gama jin duk abubuwan da suka fada. Gimbi kara tsorata tayi sai dai Anti Bebi ko a jikinta. A wulakance ta kalli Shuhada ta nunata da yatsa "Wannan fitsararriyar ma da taso nuna min ita wata ce kinga aurenta watansa shadaya na kaso mata shi. Kuma bata isa ta kara wani batare da amincewata ba. Saboda haka kema wannan kan naki da yake rawa ki daidaita shi. Idan ba haka ba uwarki Amina ma sai ta dana zawarci" Ran Gimbi ya kara baci tace "ba dai uwata ba sai dai...." Maganar bata karasa fitowa ba saboda marin da Anti Bebi ta kwasheta dashi. Dafe kumatun tayi tana zubar hawaye. Tana tsoron daga murya su Awaisu su ji me yake faruwa. Sannan ga tsoron Anti Bebi ya sake tasiri a ranta. Shuhada bata ce musu komai ba tayi gaba tana mamakin hali irin nasu. Su biyun duka abin tsoro ne gareta. Tana karasawa bakin motarsu nan ta samu su Harisu a jiki suka jingina suna hira. Su Mama kuma lokacin motarsu ta fita. Awaisu yana gani ta tsaye jikin wata motar yayi mata alama da hannu ta karaso. Bude bayan motar yayi yana mata murmushi "Kanwata shiga ki zauna kada ki gaji da tsayuwa" Daga inda take Gimbi ta hangosu taji kamar an soka mata kibiya. Anti Bebi kuwa murmushin mugunta ta bita dashi. Anya bazatayi maganin Gimbi da Shuhada ba ta hanyar sanya Awaisu son Shuhada kuma ta matsawa Alhaji ya yarda da auren. Da wannan tunanin ta shige gaban mota suka tafi saboda idon mutane. ****** Alh Mudi da Mama har suka isa gida babu mai cewa komai. Tana shiga daki ya bi bayanta da hula a hannu. "Me Bebi take yi a asibitin nan Amina?" Dama jiransa take yi don tasan sai yayi magana "nima nayi mamaki, yadda ka ganta haka na ganta" Daga murya yayi yana mata tsawa " 'Yar uwarki ce kiyi mata magana ta nesanta kanta da iyali na." Wani kallo Mama ta bishi dashi saboda haushin maganarsa da taji. "Abin da zaka fada min kenan Alhaji? Da bakina fa na fada maka irin abubuwan da Bebi take yi tun kafin ya fito fili duniya ta sani. kuma na nemi shawararka akan yanke hulda da ita saboda kare mutunci da addini." Kuka ta soma yi sai jikinsa yayi sanyi. Ya manta rabonsu da fadan da zai janyo ya daga mata murya. Amma yau saboda Gimbi da ta janyo Anti Bebi gashi iyayenta sun sami sabani. Sassauta murya yayi "Kiyi hakuri Amina, kamar yadda kika sani Gimbi tun tana karama bata son komai nata 'yan uwanta su taba. Saboda wannan halin kin sha dukanta ina hanawa. Tsoro nakeji kada dalilin zuwan surukarta ta canja hali" "Nima abin da ya dameni kenan, zanyi bincike akai amma dole ka kirata ko bayan bakinsu sun koma ne ka nuna mata bacin ranka" daga haka ta tashi zata shige ciki ko kallonsa bata yi. Alh Mudi yayi murmushi "Haba Aminatu ban sanki da fushi ba, kiyi hakuri tsawar da nayi miki" Yadda ya langabe kai sai ya tuna mata da lokutan da sanda suke da kuruciya. Dariya tayi a ranta tace Bebi ba kyau. Yanzun nan sai ta kashe aure da kisisinarta. ****** Bayan kwana biyu su Harisu suna tunanin tafiya washegari cikin dare jinin Maamu ya hau sosai likitoci suka taru a kanta. Haka suka hakura da tafiya sai sun ga an sallameta. Tsabar fargabar tafiyar mutanen Fika ne ya dameta. Duk halin Tikeke da Hinde har da Bomoi baisa taji haushinsu ba. Ganin idanunsu ya kawo sauki a zamantakewarsu da Gimbi da Awaisu. Yanzu tattalinta yake sosai yadda yake yi a baya. Ita kuma Gimbi rashin sanin me Anti Bebi ta tanadar mata yasa ta kasa sukuni. Duk irin luguden da akeyi mata a gida hankalinta baya kai. Wulakancin da ta soma na saka turaren wuta ko ta fesa na ruwa idan sun tashi daga wuri duk ta dena. Tunaninta kaf ya koma wurin neman wani bokan wanda yafi Wangesi. Idan ba haka ba kuwa tana ji tana gani Anti Bebi zata kashe mata aure ta tagayyara mata rayuwa. So take yi ta fita ma amma kullum a asibiti suke yini. Cikin dare ta kasa bacci sai juyi take yi tana neman mafita. Wata shawara ce ta tsaya mata da sassafe kuwa ta aiwatar. Dreban Anti Bebi ta kira Balele ta kwantar da kai sosai tace tana son yazo batare da saninta ba. Alqawarin dubu dari tayi masa yace gashi nan zuwa. Duk wahalar da yake da Anti Bebi bakar rowa ce da ita. Daga dubu ashirin sai talatin ke rabasu. Da yake dan hutun da aka bata na jinya ya kare tunda ga su Ummukulsum ta koma aiki yau. Office yaje ya sameta. Babu wata rufa rufa ta fada masa abin da take nema. "Idan kin shirya ko yau sai na kaiki wani kauye can jihar Neja. Mutumin bala'i ne me zaman kansa. Amma sai kin saki kudi " Gimbi tayi murmushi "indai kudi ne kada ka damu. Ko yanzu zamu iya zuwa domin a matse nake." Mukullin motarta ta bashi dama drebansu yanzu daga kai yara makaranta sai asibiti. Wayar ogansu ta kira ta fada masa jikin surukarta ya tashi tana ICU. Sunyi tafiyar awa uku sannan suka isa wani kauye. Gidan duk yara da mata. Dakin Malamin tsibbun Balele ya kaita inda ta fadi bukatunta akan mijinta da babarsa da kuma Anti Bebi. A take yace ta bashi dubu dari uku. Babu musu ta kirga ta bayar. Ya hado mata wani ruwa a jarka yace ta yayyafa duka gidan tana kiran Maamu da Awaisu a duk zubawa. Anti Bebi kuma daren yau zai karya duk wani tsafi da ta taba yi. Gimbi taji dadi sosai ta karba tana ta godiya ta fita. Balele ya koma dakin ya kalli yayansa "Kirgo min nawa nayi sauri mu tafi" Wan nasa yayi murmushi ya dauko dubu dari da hamsin ya bashi suka tafa suna dariya ya fice. A hanya ta sauke shi ta wuce gida. Ko mayafi bata cire ba ta fara aikin yayyafa ruwan dattin da suka bata. Laminde tana kitchen ta dawo saboda su Amir zasu dawo daga makaranta taji motsi. Lekawar da zata yi ta hango Gimbi tana zuba ruwan tana cewa "Safara'u! Awaisu!" Hantar cikin Laminde ta kada sosai don tsoro. Komawa tayi ta rufe kitchen din yayin da Gimbi ta shiga daki ta ajiye sauran ruwan ta fice daga gidan. Laminde ta fito ta yafa mayafinta jiki na bari. Ayatul Kursiyyu ta karanta tana ta tofawa a gidan. 'Yar purse dinta ta dauko domin daga nan gidan Mama ta nufa. Kofar gidan taji an taba Gimbi ta sake shigowa. Sako ta barwa maigadi ya fadawa Laminde yace ai tana ciki. Itama a tsorace ta dawo. Suna hada ido duk suka rude. Gimbi ta dake tace "kinji shigowata?" Bakin Laminde ya soma rawa. Hakan ya tabbatarwa Gimbi ta ga abin da tayi. "fada min nawa zan biyaki ki bar maganar nan a gidan nan" "Shawara kawai zan baki ki dena bin malamai akan Maamu. Duk duniya babu halittar da Allah Yake ambaton bautarSa tare da yi musu da'a bayan ManzonSa kamar iyaye. Me Maamu tayi miki haka kika canja har kike musu asiri" Gimbi ta kirkiro murmushin dole "kai Laminde ashe baki fahimceni ba maganin tsari ne na yayyafa saboda kariya " Laminde ta kalleta ta watsar saboda duk ta sire mata girma ya fadi, hanyar waje tayi Gimbi tana binta da sauri hankalinta a tashe. "Ki tsaya muyi magana ta fahimta. Zan biyaki sosai yadda ko kin dena aiki zaki sami jari" Sauri Laminde ta kara tana bude gate Gimbi a gigice don bata san ina zata ba ta cewa mai gadi ya kamota. Jin umarnin da aka bashi akanta yasa ta kwasa a guje sai dai bata duba titin nasu ba mota ta taho da gudu tayi gaba da ita sai jini ne ya wanke wurin. *KASHE FITILA*💡20 *Batul Mamman*💖 Wata muguwar kara Gimbi ta saki tare da dora hannu a ka ganin yadda jini yake bin jikin Laminde. Duk abinta tana tsoron yin kisa. Mai motar ya tsaya ya fito a guje shima yana fatan Allah Yasa baiyi kisan kai ba. Motoci ne suke tsayawa ganin yadda jama'a suka fara taruwa a wurin saboda gidan nasu a bakin titi yake. Ana kokarin sanya Laminde a motar mutumin da ya bugeta sai ga 'yan sanda biyu daga wurin junction din da ake bayar da hannu. Tambayoyi suka danyi na sanin wacece sannan sukace a wuce asibiti. Sai da suka isa National Hospital sannan Gimbi hankali ya fara tashi da irin tambayar da suke mata. Daya cikin 'yan sandan yace a cikin 'yan kallo wani yace biyota akayi ko me zata ce game da hakan. Nan fa ta kara rikicewa tana nemarwa kanta mafita kada asirinta ya tonu. Karya ta sharo a take a wurin irin wadda ko Laminde tayi rai baza'a yarda da abin da zata ce ba tunda mai aikice. "Ai na fada muku mai aikina ce. Sata na kamata zatayi min shine ta gudu" Dan sandan yace "kina da shaida akan hakan?" "Tambayi mai gadi shi nace ya tsayar min da ita" "Zamu jira likitan ya fito domin ji daga bakinta" ***** Zaune Awaisu yake yana sa hannu a wasu takardu Ummukulsum ta kira shi. Gabansa har dan faduwa yayi kafin ya daga yana tsoron ko jikin Maamu ne. Muryar Baaba yaji da alamun bacin rai "Anya Awaisu kai da matarka kuna kyautawa kuwa? Ace mara lafiya tun abincin safe har yanzu shiru " Ajiye biron hannunsa yayi ya mike tsaye "Baaba ina Laminde?" "Kaniyarka, Laminde kake aure? To tun dazu ta tafi don sauri ko dreba bata jira ba baiwar Allah tace zata jira yara su dawo ta bayar da abincin. Kuma su Tikeke ma gida zasu koma idan an kawo saboda likita yace muna cika dakin" Hakuri ya bata sannan ya kira Gimbi. A lokacin tana ta tararrabin farkawar Laminde da abinda zata fada sai waya ta shigo mata. Har wani zabura tayi don tsoro. Yana kira yaji wayarta busy. ***** Sunan Ogansu ta gani. Jiki a mace ta dauka tana tunanin karyar da zata sake yi masa. "Mrs Awaisu kin tayar mana da hankali. Sama da awa hudu kince mother in-law dinki tana ICU. Ina ta kira tun dazu baki dauka ba" Yawun bakinta taji ya kafe ta kasa magana. Shi kuwa ya cigaba. "Da naji shiru na kira maigidan naki" Bata san lokacin da ta daga murya ba "Ka kira wa??? Ya dauka???" "Ban same shi ba shiyasa na sake kiranki. Idan mun tashi zamu biya asbitin mu dubata ni da sauran staff." Kafin ta tattaro kalmomin da zatayi amfani dasu domin dakatar da zuwan nasu ya kashe wayar. Ji tayi gabadaya duniyar tayi mata zafi. Kiransa take shirin yi sai ga ba Awaisu ya shigo. Dan sauran kuzarinta a take ya kare taji cikinta ya duri ruwa. Tana amsa kiran ta jiyo muryarsa kamar zata fasa mata dodon kunne. "Wane irin wulakanci kike yi min ne? Kin barmin uwa da baki a asibiti babu ke babu Laminde. Wannan aikin naki wanda na lura duk tsaurin banki kin mayar dashi wurin gantali shi zan hana kowa ya huta" Ita mamaki take yi yadda ta kashe kudi har dubu dari hudu lokaci guda amma komai ya rikice mata haka. Sauke murya tayi har ta fara saduda "Muna asibiti da Laminde" Wani mugun tsaki yaja "to kiyi maza ku karasa dakin a kai musu abinci. Yau ni da ke ne wallahi idan na dawo. Sai kin fada min what you have against my family" Tuni ta amincewa ranta Anti Bebi tasa Wangesi ya warware sauran aikinsa sannan an kara mata da na bakinjini. Bayani tayi masa na inda suke yayi saurin fitowa babu shiri. Abinci ya tsaya ya sayawa su Maamu sannan ya wuce asibitin. Bayan yaje ya fada musu inda zashi tare da Harisu sannan ya kira dreba akan yazo ya dauki su Maman Rumana zasu je suyi girki bayan sun gama cin abincin. Asibitin da aka kwantar da Laminde suka wuce. Suna zuwa ya wuce emergency inda Gimbi tace likita na duba ta, ga kuma police a gefe. Da isarsu likitan ya fito ya sanar dasu an samu jinin da take zubarwa sakamakon wani karfe a gefen titi da ya soke mata cinya ya tsaya. Sannan ta sami karaya a hannu ga kuma fuska da ta kumbura saboda buguwa. Bayan ya tafi Awaisu ya kalli Gimbi tana ta rarraba idanu. "Abin da ban fahimta ba shine me ya kaita fitowa bayan dreba ne yake mayar da ita idan ta gama girki" Shiru tayi babu amsa. "Baki ji me nace bane? Wai ke ma din me kike yi a gida a wannan lokacin. Kina maaikaciyar banki amma sai kiyi ta yawonki son rai" Tsoron kada ya dawo da fadan kanta tace "kamata nayi a dakinka zata yi sata. Shine da ta ganni ta fito da gudu har hakan ta faru" "Laminden?, shekara biyu da rabi bata taba sata ba sai yau?" "Karya kake nufin ina yi mata ko me? Ka bari ta farka ka tambayeta mana" Harararta yayi yana ji a jikinsa karya take yi masa. "Dazu na tambayeki babu amsa. Nace me ya kaiki gida lokacin aiki?" Kafin ta samu karyar da zata yi masa Harisu ya janye shi gefe. "Wani sabon salo ne ka fito dashi na yiwa matarka fada ko bakaken maganganu a gaban mutane? Ba daidai bane iyalinka tayi maka laifi ka rasa wurin tsawatarwa sai bainar jamaa" "Yaya wallahi tun ranar da kuka zo na rasa dalilin da yasa nake jin haushinta. Amma idan ka duba zaka ga da gaske laifin take yi. Gani nake kamar tana boye min wani abu" Tausayi ya bawa Harisu hakan yasa ya dafa kafadarsa. "Kada ka bari zamanku na shekaru ya baci a yanzu da kuka tara iyali. Idan Allah Yasa Maamu ta warke komai ya daidaita mun tafi ka samu kuyi magana ta fahimta." Shawarwari Harisu ya cigaba da bashi ita kuma Gimbi tana gefe ranta ya gama baci. Ba komai ke damunta ba sai tunanin Harisu ne yake ingiza Awaisu yana mata wulakanci yanzu. Ji tayi komai ya dagule mata ta fice daga wurin. Balele ta kira zata yi korafin rashin ganin sakamakon aikin bokansa. ***** Anti Bebi na mota tana jiran Balele da yake tsaye ana zuba mai taji wayarsa na kara. Daukowa tayi zata mika masa ta taga ta kula an rubuta *hajiya gimbi*. Wata irin dariya ta fashe da ita daga Balele har mai zuba man sai da suka tsorata. Yana shiga motar ta bukaci ya fada mata meye hadinsa da Gimbi. Sanin hatsabibancin uwardakin nasa yasa ya fada mata komai. Cinya ta daka tana tafa hannuwa "lallai Gimbi tana cikin matsi. Shine don wulakanci ka kaita gidanka. To bata ga yaranka ba gari guda." Dukar da kai yayi kada tace ya dawo da kudin. "Wannan kudi kaci rabonka a jikinta. Neman boka yanzu ta fara ma. Wani abin sai na kamata a hannu. Bari dai Shuhada ta gama idda " Balele ya zaro ido "Hajiya me zaki sake yiwa Shuhadan? Da kin barta haka tunda auren ya mutu" Yana tausayin yarinyar ganin yadda Anti Bebi ta juya musu rayuwa ita da iyayenta lokaci daya. "Aure zanyi mata ba wata tsiya ba" ***** Bayan Laminde ta farka kumburin bakinta ya hanata magana. 'Yan sandan suka ce zasu dawo washegari. Awaisu yasa Gimbi ta kira wadda ta kawo mata ita domin a sanar da danginta. Da ma bazawara ce, danta daya Nafi'u dan kimanin shekara sha bakwai saboda tayi auren wuri. A hannun kanin babansa yake tun bayan rasuwar mijinta. Da suka ji sakon Nafi'u ya sha kuka suka yi shirin zuwa Abujan shi da kawunsa. Kawun nasa kuma yayi alqawarin ta dena aiki kenan. Gara ta nemi wata sanaar a kusa da gida. ***** Washegari har yamma Laminde babu bakin magana. Mutanen Fika sun je dubiya tare da Maamu wadda aka sallama a ranar aka bar Hinde a wurinta. Mama itama ta kadu da jin wannan mummunan labari taje ta dubata tare da wata mai aikinta wadda zata rinka kwana da ita. Nafi'u da Kawunsa sunzo inda Awaisu yayi ta basu hakuri. Suma a gidansa sukayi masauki. Kawun yace ana sallamarta gida zasu tafi da ita. 'Yan sanda kuma jira suke ta fara magana su dauki jawabinta. **** Su Maamu na zuwa gida Baaba tace zasu koma Fika washegari tunda sun kwana biyu. Maamu ta rasa yadda zatayi. Tana son fadawa Baaba matsalarta a gidan Awaisu amma tana son rufa masa asiri. Da kunya ta kare rayuwarta a alfarma duk da sun dauketa tamkar jininsu. Ita da take burin Awaisu ya cigaba da kyautata musu ace kuma ita kanta ya gagara rikonta. Gashi bata da 'yar uwa mace da zata iya fadawa domin neman shawara. Tana ji tana gani washegari suka tafi. Tikeke da Hinde duk tijarar da suka tanada abubuwan sa suka faru a gidan suka sa su yin lakwas. Bomoi kuwa yayi alkawarin dawowa nan da dan lokaci cin arzikin gudan jininsa. Suna bakin mota Rumana tana ta kuka har Gimbi na zolayarta wai ta zama 'yar yaye. Ita wasan ma tsoro ya bata don bata saba ba. Dayake tafiyar sassafe ce suna tafiya itama da yaran dreba ya kaisu makaranta. Bandaki ta tafi ta rufe kanta tana kuka. A nan Yusra ta sameta. Bayan tambayoyi da kyar ta sanar da ita komai game da zamanta da kawunta. "Da nice ke Rumana da tuni kowa ya manta na taba zaman Abuja. Ai wallahi da haukan gaske da na karya zan gudu. Rannan Umma take cewa na tambayeki ko baki da lafiya kike ta ramewa ashe yunwa ce. Kuma kika ki fada min" ta kare da hararta. Rumana bata amsa mata ba, hankalinta ya tafi tunanin maganar Yusra...anya ba haukan zatayi musu ba kuwa. Har fargaba take a tashi ta koma gida. ***** A tsattseye suke gefen gadon da Laminde take tare da 'yan sanda biyu sai Awaisu da Gimbi da kuma Kawu da Nafi'u. A hankali saboda kumburin bakinta Laminde ta tashi da salati. Tana hada ido da Gimbi ta razana ta fara cewa "ruwan asiri" Kasa kunne duk suka yi domin gane me take fada. *KASHE FITILA*💡21 *Batul Mamman*💖 Laminde ta sake cewa "ruwan asiri" Gimbi ji tayi kamar an sauke guduma a cikinta ganin Laminde zata tona mata asiri. A daidai lokacin Mama ta shigo kuma ta ji abin da Laminde ta fada. Kawu ne ya kara matsawa bakin gadon zaiyi mata tambaya sai daya daga cikin 'yan sandan ya dakatar dashi. Da sauri Gimbi ta kirkiro kuka harda hawaye. Ita kanta mamakin saurin zubar hawayen nata tayi. Kan Laminde ta fada tana rusa kuka "Abban Haris kaji wata masifa, Laminde ba dai tabin hankali kika samu ba" Nafi'u ya matso da sauri yana tambayarta ko ta gane shi. Gimbi ta samu yana tayata kukan duk ta cika dakin da karaji. "Yallabai ku nemo mutumin nan da ya kadeta. Wallahi bazamu yarda ba idan ta haukace" Tsawa Awaisu ya daka mata ganin itama ta zama kamar mahaukaciyar "Meye yake damunki ne, dubi tana son yin magana kin hanata" Ko motsi batayi ba domin tasan muddin Laminde ta fadi abin da ta gani kowa yarda zaiyi. Musamman Awaisu da ta kula yanzu kamar ma ya tsaneta da Mama da take saka mata ido. 'Yan sandan suka ce kowa ya fita zasuyi mata tambayoyi. Gimbi ta wani kankame Laminde "Babu inda zani sai na tabbatar da lafiyarta. Laminde amana ce garemu. Ni satar da na kamata zatayi min na yafe. Ki yafe min, duk laifina ne da na kasa hakuri ban saurari dalilin da yasa kika shigarwa Abban Haris daki ba" Maganar ta doki kunnen Laminde cikin kaduwa, _sata!_. Yanzu sharrin sata Gimbi ta kala mata. Hawaye ta soma yi tana kallon danta wanda aka zubar mata da mutumci a gabansa. Sake bude baki tayi zata fadi gaskiyar abin da ta gani Gimbi kawai ta mike tsaye tana dafe kai "Wayyo kaina, washhhh" Sai gata ta fadi a kasa gaban Kawu. Duk abin Awaisu da gudu ya fita neman likita. Mama wadda tun shigowarta bata ce komai ba sai lokacin tayi wani murmushi mai ciwo. Iyakar abin da Gimbi tayi a gabanta yanzu ya tabbatar mata da gaskiyar Laminde. Fita tayi jiki a sanyaye tana bakincikin wannan al'amari. Tana shiga mota ta sanar da dreban inda zai kaita. ***** Da gaske Gimbi taki farfadowa har kusan rabin awa. Likitan ya rasa gane mene ne yake damunta. Da ya auna jininta ya ga ya hau. Awaisu yayi wa bayanin cewa a kula da ita domin ciwon Laminde ya tsaya mata sosai. 'Yan sanda suka gama bincikensu suka tafi. Iya abin da Laminde ta fada bai wuce cewa ba sata tayi ba kuma bata shiga dakin maigidan ba. Bayan fitarsu Kawu ya tilasta mata ta fada masa gaskiyar me ya faru. Tana fada tana kuka tace dole zata sanarwa Mama. "Laminde mutanen nan ba sa'aninmu bane. Wannan matar idan har gaskiya kike fada tafi karfinmu ta ko ina saboda haka ki bar maganar nan" Kokarin zama tayi Nafi'u ya tayar da ita sosai "iyalin mutumin nan musamman mahaifiyarsa suna cikin hatsari. Da ace kana ganin irin yadda uwar mijin take rayuwa a gidan bazaka ce nayi shiru ba. Ba sharrin sata ba ko me zata yi min sai na fadawa 'yan sandan nan gaskiya" Kafin Kawu ya bata amsa yace Nafi'u ya basu wuri. Ya kama kofar zai fita Gimbi ta shigo fuska cike da hawaye. "Laminde ki rufa min asiri. Abubuwan da kika gani sharrin shaidan ne. Kada ki tona min asiri ki raba sunnar Annabi SAW. " "Kinga Hajiya daga nan garinmu zamu wuce da ita. Ina rokonki da kiyi hakuri ki janye satar da kika dora mata. Daga yau kin dena ganinta ma" Farinciki ne ya bayyana a fuskar Gimbi har ta kasa boyewa Kawu. Kudi ta debo a jakarta ya dakatar da ita ta hanyar daga mata hannu. "Bama neman komai daga gareki. Kina iya tafiya amma kada ki taba mantawa rana dubu ta barawo...." Dan dakatawa tayi tana auna maganarsa sai kuma tayi saurin fita saboda Awaisu yana wurin likita ta fito daga dakin da aka bata. Laminde ta kalli Kawu zata yi magana yace ta bar komai a hannunsa. Irinsu Gimbi baka musu fito na fito lokaci guda, musamman idan baka da shaida. Zaiyi iya kokarinsa wurin taya Awaisu da mahaifiyarsa da addu'ar neman tsari. ***** Naman kaza take ci tana kurbar juice a kofin glass taji an banko kofar dakinta. Duk gidan hatta Shuhada da take iya yi mata rashin kunya wasu lokutan bata isa tayi mata haka ba. Shiyasa tana jin karar kofar ta zabura ta tashi. Kusan karo suka yi da Mama kafin taji saukar mari zazzafa a kuncinta. "Bebi sai Allah Yayi mana shari'a ni da ke. Me nayi miki haka kika lalata rayuwar 'yata" Duk da radadin da kumatunta yake yi bai hanata dariyar keta ba. "Su Aminatu salihan bayi. To ai kinsan ba'a daya a dangi. Wannan Gimbiyar taki kina ganinta haka ba karamar fitinanniya bace." Mama ta kara harzuka "kada kiyi tunanin zan bar maganar nan haka. Naji komai daga wurin Laminde. Nasan kece kika kaita wurin shaidanun bokayenki." "Kin kuskuro 'yar uwa. Wannan karon Gimbiya gaban kanta tayi. Shawara ta daya gareki shine ki nemi Awaisu ya mayarda uwarsa garinsu. Idan ta cigaba da zama to ina mai tabbatar miki yanzu ta fara kwanciya a asibiti. Gimbi ba karamin tsana tayiwa wannan matar ba" Kallonta Mama tayi sosai. Anti Bebi ko kadan zuciyarta bata rissina ga abin da tayi niyya. Idan aka cigaba da haka watarana ba auren Gimbi ne kadai zai mutu ba. Su ma iyayenta mutumcinsu sai ya zube a idanun al'umma. "Bebi ki dubi Allah ki kyale Gimbi tayi rayuwarta. Idan tazo gidanki kici mutumcinta ki koreta. Ke kin sani bin boka da malaman tsibbu haramun ne amma kike takewa. To akan mene ne sai kin hada da 'yata?" "Masu 'ya manya, abin da nake so ki sani shine yaran yanzu idanunsu a bude suke. Kowa ya waye da sanin rayuwa. Idan baki nemi taimako ba kina kallo bakincikin da namiji zai kasheki a banza. Ko zaki ce kin manta irin bacin ran da Innarmu tasha wurin Baba? Tun lokacin nasan cewa namiji zuma ne sai da wuta. Ban ga wani shegen da zan ragawa ba yazo yana cin zarafina" Mama ta saki baki tana sauraron kanwarta da tayiwa duniya gurguwar fahimta. "Ba duka aka zama daya ba Bebi. Yanzu kina jindadin zama da mijinki ya zama kamar hoto sai yadda kika juya shi?" "Wannan ne mulkin, ko da wasa bai isa ya takani ba. Gimbiya kuma ki dena ganin laifina ita ta kawo kanta. Mata da dama a zamanin nan sai da haka suke samun damar cimma burinsu a wurin mazajensu. Me za'ayi da uwarmiji banda takura da sanya idanu" Anti Bebi tayi nisa. Mama gani tayi cigaba da yi mata magana bacin lokaci ne sai kawai ta juya ta fita daga gidan. Ba abin ta fadawa Innarsu ba tasan babu wani mataki da zata dauka. Komai Anti Bebi tayi daidai ne. Tana zuwa gida ta kira Alh Mudi a waya ta fada masa. Ya rinka fada kuwa kamar ya ari baki. Allah Yasa yana gari yace ta kira masa Gimbi kafin ya karaso gidan. ***** Sai yamma Gimbi ta sami damar amsa kiran Alh Mudi. Lokacin ta tabbatar Laminde da 'yan uwanta bazasu cigaba da zama barazana a gareta ba. Shi kuma Awaisu ya wuce kasuwa. A tsorace ta shiga gidan domin tun fitar Mama daga dakin asibitin jikin Gimbi ya bata akwai matsala. Sama ta hau dakin Alhajin ta samesu duka su biyun babu wanda yayi mata kallon arziki. Haka ta sami wuri ta zauna can gefe. Alh Mudi ne ya fara magana "Gimbi ki fada min tsakaninki da Allah mijinki yana tauye miki hakki ne?" A hankali ta girgiza kai alamun a'a. Ya sake tambayarta "Ita Maamu ko sau daya ta taba nuna bata sonki da danta?" Wannan karon ma girgiza kai tayi. A take ta ji Alhaji ya daga murya ya soma fada. "Bakin gwargwado Gimbi mun baki tarbiya daidai iyawarmu. Mun baki ilimi domin ki bambance daidai da abin da yake ba daidai ba. Amma sai kika zabi biyewa son zuciya da hudubar shaidan. To ki sanu komai ka shuka da sannu zaka girbe duk daren dadewa" Da yake ba kunya gareta ba sai ta dago kai tana tambayarsa me yake faruwa ne. Hakan ya kara batawa Mama rai ta tashi zata kai mata duka. Alhaji yace ta zauna "Bar ta Amina, Gimbi duk abin da kike yi domin ganin Maamu ta bar gidan danta mun gane. Banyi zaton akwai ranar da zan wayi gari 'yar cikina tana mu'amala da malaman tsibbu ba. Saboda haka na shirya sanar da Awaisu halin da ake ciki zan kuma umarce shi da ya sakeki muddin baki chanza hali ba" Da sauri ta dago kai tana kallon iyayenta. "Alhaji saki fa kace." "Rufa min baki mara kunya, har kina da bakin magana. Alhaji kace ya saketa kawai ya huta. Idan kina son shi da gaske babarsa ko musaka ce wallahi zaki taya shi kyautata mata" cewar Mama Gimbi ta matso kusa da Mama jin abin da tace tana kuka "don Allah kuyi hakuri bazan kara ba." Fada sosai suka rinka yi mata tare da cigaba da barazanar zasu saka Awaisu ya saketa. Da suka ga hankalinta ya tashi sosai shawarwari suka bata da nasiha akan hukuncin da zata tarar nan gaba a lahira. Ita dai rokonsu takeyi kada Awaisu yaji maganar. Da ta fito daga gidan ko tunanin kirki batayi ta wuce gidan Anti Bebi. Da kuka ta shiga ta fada jikinta. Anti Bebi ta tureta tana fadan me ya kawota gidan. "Ki taimakeni Anti Bebi kada su Mama su kashe min aure. Awaisu shine farincikina. Komai nawa ya rikice tun bayan rabuwarmu a asibiti." "Gimbiya kenan, ai nayi zaton karanki ya kai tsaiko har zaki iya hada kafada dani" A ladabce ta kalli Anti Bebi "kiyi hakuri, bana son duk wani abu da zai gifta tsakanina da Awaisu mara dadi. Yanzu baki ga irin wulakancin da yake min ba. Gashi su Mama sun gano" Anti Bebi tayi murmushin samun nasara akan Gimbi. Lallai Wangesi ibilishi ne. Cewa tayi kawai yayi duk yadda zaiyi Gimbi ta dawo karkashin ikonta. Gashi ta gani kuwa. "Yanzu me kike so ayi?" Da yatsu ta fara kirgawa "so nake Awaisu ya koma kamar mijinki, kada ya rinka min musu ko gardama, Maamu ta koma garinsu ko kuma ya fita harkarta ni kuma zanyi yadda na ga dama har sai ta tafi don kanta, su Alhaji su dena yi min fada duk abin da zanyi babu ruwansu, sannan a wurin aiki kowa ya rinka shakkata hatta oganmu" Ita kanta Anti Bebi ta jinjinawa dogon burin Gimbi. Shiyasa baa so mutum ya fara shige shige. Idan akayi rashin sa'a imani yayi karanci shikenan kuma an soma kenan. Ko don ta rama marin da Mama tayi mata zata karbi Gimbi hannu bibbiyu. Amma kuma tayi alkawarin sai itama tayi kuka a gaba. Bata ga wanda ya isa ya takata ta kyale ba. Bayan tafiyar Gimbi dakin Alh Maitama ta shiga. Yana zaune shi kadai a takure a gefen gado kamar wanda akace kada ya motsa. Yana ganinta ya sake gyara zama. Sakin fuska tayi bayan yasan dazu ya bata mata rai saboda ta nemi kudi yace ta jira ayi albashi. Shine tace ya zauna a daki. Sassauta murya tayi tana masa murmushi "Alhajina yaushe Shuhada zata tafi ne?" "Ke nake jira dama ki fadi rana sai na sanar da ita. Kamar yadda kika nema na hanata fitar" "Na samar mata miji ne. Idan ta gama idda sai ayi auren." Kamar yayi magana sai ya kasa saboda bakinsa da yayi masa nauyi "Baka ce komai ba, ko banyi gwaninta bane?" Dolensa ya kirkiro murmushi "kinyi min komai Bebi, nagode sosai." Tashi tayi har ta fita tana jiyo muryarsa yana mata godiya. Tana zuwa daki ta dauki waya ta kira Wangesi. Duk bukatar Gimbi ta zayyana masa sannan ta kara da cewa bata so Alhaji Maitama ya bar Shuhada ta tafi. Kuma tana gama iddah ayi aurenta da Awaisu ko ta wane hali ne. *KASHE FITILA*💡22 *Batul Mamman*💖 *Bayan sati uku* Babu kowa a ajin kasancewar ko bakwai da kwata batayi ba. Rumana ta shigo kayan makarantarta kamar an kwato a bakin kare. Sun yamutse gashi da alamun ko wanki basu samu ba. Zama tayi akan kujerarta ta hada kai da teburin gabanta tana kuka. Tunda take a gidan kawunta Awaisu bata taba ganin wulakanci irin na safiyar yau ba. Ji take yi kirjinta kamar ya fashe don bakinciki. Shi kuwa Awaisu ya fice fit daga ranta bata ko kaunar ganinsa. Tana wannan kukan wasu mutum biyu suka shigo taki dago kanta balle a ga idonta. Yusra ce ta hudun shigowa ajin. Ko ba'a fada ba tasan aminiyarta ce a zaune shiyasa tana ajiye jakarta ta kai mata dundu a baya. Maimakon ta dago tace zata rama yadda suka saba sai taji shiru. Dago kan Rumana tayi da karfinta sai ga hawaye suna sintiri a kumatunta. "Rumana kiyi hakuri, ko zaki rama ne?" A zatonta dundun da tayi mata ne yasata kuka. Ganin an fara kallonta yasa ta fice daga ajin Yusra na bin bayanta. Bayan SS3 da babu kowa saboda daliban sun gama WAEC suka je. Nan Yusra ta rinka rokon Rumana da kyar ta fada mata irin zaman da takeyi a gidan kawunta da kuma sabon salon wulakancin da ake yiwa Maamu. "Yanzu ita matar Uncle din naki don wulakanci idan ita ce aka yiwa haka zata ji dadi?" Rumana ta goge idonta da yake faman radadi saboda kuka "Don ma ba a gabanki akayi bane Yusra." "Ni shawara daya zan baki wallahi ku tattara ku koma gida. Ki fadawa Maamu tace zata koma Fika. Idan kuma taki Allah kiyi tafiyarki. Ga yunwa ga wulakanci....tabdi, wallahi da nice watarana sai na zuba mata miyar danyar kubewa a bakin kofa tayi zumulmula." Dariya ce ta kwacewa Rumana harda kyakyatawa. Amma har suka koma aji zuciyarta tana mai kara samun karfin gwiwar aiwatar da shawarar kawarta. ***** Maamu ke zaune a daki ita kadai. Irin yadda take ji a zuciyarta ko kuka tayi bata tsammanin samun sassauci. Ta rasa me ta tsarewa Gimbi har take yi mata irin wannan cin kashin a cikin gidan dan da ta tsugunna ta haifa. Kwanakin baya da tayi rashin lafiya Awaisu ya dawo mata yadda yake a da. Tattali da mutuntawa da ya dace da mahaifiya babu inda ya rage ta. Lokaci guda kuma kamar anyi ruwa an dauke. Shigowa dakinta ya gaisheta dama har ta hakura. Abin da yafi damunta bai wuce yadda Gimbi take mata wulakanci a kan idonsa ba amma kallon wayarsa ko tv yafi masa mahimmanci. Tunawa tayi da yadda suka rabu da safe taji wani siririn hawaye yana bin idonta. Rumana Gimbi ta sa firar dankali mai yawa irin kananun nan masu cin rai tun dare. Bata kwanta bacci ba sai daya saura. Karfe biyar ta tashi yaranta ta aiko Daula ta tashi Rumana. Cike da fitsara tasa kafa ta hauri Rumanan da take bacci a kan abin sallah a ciki, caraf a idon Maamu. Ta kuwa kai mata duka tana mata fadan abin da tayi. Daula ta bude baki ta saki wata irin kara kamar wadda aka sokawa wuka. Da sauri Gimbi ta shigo tana tambayarta me aka yi mata. Maamu bata ma san da yarensu take magana ba don haushi ta nuna mata Rumana rike da ciki tana sanar da ita me ya faru. Gimbi ta wani kankance ido "ke dallah ba ke na tambaya ba sai son zance ke da ba'a gane yarenki" Maamu har dan firgita tayi da tsawar, ita kuwa Rumana jikinta yayi sanyi don abu ne da bata taba gani ba yiwa babba tsawa. Kafin ta gama tunani taji Gimbi ta rike mata kunne ta murdeshi sosai. Rumana sai kuka tana kokarin kwacewa. "Mummy kiyi hakuri" ta fada da kyar "Ke kuma idan kika sake taba min yara sai jikinki ya gaya miki. Kuma daga yau sai yau kada ki kuma kirana Mummy. Uwarki na kyauye kwadayayyu masu kama da may..." Kasa karasawa tayi saboda shigowar Awaisu. Maamu tayi saurin fada masa yadda akayi "Kace matarka ta sakar min jika haka. Ba Rumana bace ta daki Amina nice na dake ta" Ya juya ya tambayi Daula ta gyada kai tana cigaba da kuka. Gimbi ta saki Rumana kunnenta yana radadi kamar ya tsinke. Awaisu ta kalla fuskarta babu alamun wasa. "To ka yiwa Maamu magana wallahi babu ruwanta da yarana. Duk ta bi ta tsanesu kamar ba ita ta haifeka ba" Daga shi har Rumana shiru sukayi na dan lokaci. Sai daga baya kamar an tsikare shi ya hau Maamu da fada yana jaddada mata bai ga wanda ya isa ya taba masa yara ya kyale ba. Yana gama fadan ya fita daga dakin. Gimbi ta galla musu harara ta bi bayansa. Da suka gama shiri Rumana ta fito ta kwashe kayan da sukayi amfani dasu ta wanke kamar yadda Gimbi ta shardanta mata kullum kafin ta tafi makaranta. Tana cikin wankewa Amir ya shiga kitchen din da nasa kofin tea din ko rabi bai sha ba. Jin muryar Gimbi kuma yasan zata masa fadan kin shanyewa yasa shi saurin jefa kofin cikin sink tea din ya watsowa Rumana a gaban hijab da rigar makaranta. Ta bude baki zata yi magana sai ta tuna yadda akayiwa Maamu shiyasa ta fasa. Wannan dalilin yasa ta dauko dayan uniform din a kayan wanki ta saka saboda yadda wancan ya baci. ***** Ana tashi daga aiki Gimbi ta wuce gidan Anti Bebi. Yanzu sun kara dinkewa sosai. Gimbi ta ma dena tsoron me su Mama zasu fada. Harkar gabanta kawai take yi. Yau ma labarin yadda tayiwa Maamu da Awaisu da safe taje bata. Anti Bebi tayi dariya sosai da taji labarin. "Me akayi akayi maza dama...dadin aure fa a zamanin nan bai wuce ki wawuri duk abin da zaki iya a hannun dan iska ba. Mazan yanzu kina tarairayarsu da ladabi da biyayya suna kunsa miki bakinciki da ciwon zuciya. Mace na shekara a gidan miji sai ki ganta a layin karbar maganin hawan jini" Dariya Gimbi tayi suka tafa da Anti Bebi "Kuma fa hakane, kawayena biyu duk kafin haihuwar fari sun kamu da hawan jini. Nagode da kika bude min ido wallahi. Mijin da nake aure ma yayi kadan ya daga min hankali bare wata tsohuwa" Faffadan murmushi ne ya bayyana a fuskar Anti Bebi "Da kyau Gimbiya. Da ace mata sun fahimci meye aure da bakincikin da namiji bai kashesu ba" Hira suka sha sannan Gimbi ta tashi ta tafi gida ana kiraye kirayen sallar Isha. Lokacin Rumana ta dawo ta gyara gidan tsaf sai dai baa bata izinin shiga store ba bare girki. Da abinci a leda Gimbi ta dawo ta bawa yaranta. Bayan sun gama da kanta ta tukawa Awaisu tuwo ta dibarwa Maamu da Rumana dan kadan a kwano daya wuraren goman dare. Suna ci Maamu dan kadan take tsakura saboda Rumana ta koshi. Haka suka gama cikinsu babu nauyi sai ruwa da suka sha sosai domin kada yunwa ta hanasu bacci. Shadayan dare Awaisu ya dawo a gajiye. Ko hanyar dakin Maamu bai kalla ba ya wuce nasa. Gimbi don zolaya harda cewa ko zaije taya Maamu hira yau. Rai a bace yace bata ganin yadda ya gaji. Murmushi tayi tana bashi hakuri shi kuma yana wani hade rai. ***** Haka rayuwa ta juyawa su Rumana. Kullum da fargaba suke tashi domin yanzu Gimbi bata boye musu mugun nufinta. Burinta kawai su bar gidan taci karenta babu babbaka. **** Kwanan Shuhada biyar da gama iddah. Anti Bebi harda dauko wasu mutane wai malamai ne zasuyi mata adduar neman tsari. Alh Maitama kamar kullum bashi da bakin magana sai ma godiya gareta saboda kula da yarsa da taje yi. Suhail ya gama jarabawa amma rashin kudi a hannunsu yasa Shuhada tace ya zauna kawai har a koma hutu ya cigaba da karatunsa . Daga dakinta ta fito zata kwaso kayan shanyarta don mai wankin gidan daga na Alhaji sai Anti Bebi yake wankewa. Daya daga cikin malaman karyar ne ta gani da Anti Bebi a wani karamin falo suna magana a hankali ta lallaba ta tsaya a gefe babu mai ganinta. Daga ciki take jiyo muryarsa a hankali "Wannan maganin Wangesi yace ki zubawa ita babar taki a abin sha. Yadda zata shanye haka duk wani fushi ko bacin ran da zaki haddasa mata zata shanyeshi tas" Juya maganin tayi tana dan murmushi. "Shi Alhajin yace na barshi haka ko" "Yaji tsoron kada yawan asirin ya haukata shi shine yace a saka masa ido na dan lokaci" Dafe kirji Shuhada tayi don tasan da babanta ake. Barin wurin tayi niyar yi taji mutumin ya ambaci sunanta. "Ita yarinyar nan Shahada take ko me ga nata maganin. A abinci zaki zuba taci. Da zarar taci yace ko sunan mutumin kika kira sai taji gabanta ya fadi sonsa ya karu a ranta. Ki kwantar da hankali bazata yi musu ba har ayi auren" Karbar wannan magani yasa Anti Bebi nishadi da murna sosai. "Sai na koya musu hankali su duka. Awaisu dama nasa matarsa ta gama juya masa tunani. Abin da ya rage bai wuce na aura masa Shuhada ba kuma na tsaya mata har sai ya saki Gimbi. Ni da ka ganni nan bana yafe rashin mutumci ko kadan" "Kiyi yadda yace zaki ga biyan bukata" Daga haka ta karbi maganin kafin su fito Shuhada ta bar wurin da sauri. Dakinta ta koma ta hau kuka. Ta rasa wace irin mutum ce Anti Bebi. Share hawayenta tayi ta shiga tunanin neman mafita. Wurin rabin awa ta kwasa a dakin kafin ta fita. Kitchen ta dosa dauko abinci ta tarar da Anti Bebi a falo. "Ke ina zuwa?" "Abincina zan dauko ko shima an hana ne?" "Aa Shuhada, ni bana jindadin yawan rigimarmu kamar ba mata ba. Ga abinci can akan dinning table kije kici." Ba musu Shuhada ta wuce ta diba ta cika plate har yayi tsororo. Hanyar dakinta ta nufa Anti Bebi tayi dariya "Shegiya mai cikin zani. Baki iya komai ba sai ci da kashi. Ji wannan tulin abinci kamar mai aikin karfi" Shuhada tayi kamar bata ji ba ta wuce. Leda ta samu a gabanta tana juye abincin cokali cokali kamar ci take. Ba zato taji an turo kofar dakinta. Anti Bebi ke son tabbatarwa ko taci. Ita kuwa Shuhada sai ta wayance tana kokarin kai cokalin baki. Anti Bebi bata ce komai ba ta juya ta fita. Shuhada ta juye fiye da rabin abincin a leda sannan ta mayar da sauran kitchen. Anti Bebi ce ta biyota har kitchen ta dafa mata kafada. Shuhada don tsoro kamar ta saki fitsari. Bata kaunar hada inuwa da ita. Ji tayi Anti Bebin tace "Kina son Awaisu mijin yar nan tawa Gimbi?" Da kyar ta iya hadiyar yawu kafin ta tattaro hankalinta ta nutsu. Kai ta sunkuyar ita a dole kunya take ji tayi murmushi "Kai Anti har kin gane" Anti Bebi tayi wani juyin farinciki sannan ta sake maimaita tambayar. Wannan karon Shuhada hannu tasa ta rufe idanunta tana wani fari "Ni dai Anti kunyarki nake ji" Daga haka ta kwasa da gudu ta bar kitchen din. Anti Bebi taji dadi mara misaltuwa ta kama dariyar mugunta. Da Shuhada zata wargaza rayuwar Gimbi. Shuhada na shiga daki rufe kofar tayi tana numfashi da kyar. Tunda ta tari Anti Bebi da wannan karyar ya zama dole tayi amfani da wannan damar wurin sanin sirrinsu da kwatarwa kanta da duk wanda suka kafawa takunkumi 'yanci. [15/08, 17:45] ‪+234 803 272 5896‬: *KASHE FITILA* 23 *Batul Mamman*💖 _*Waiwaye*_ _Shuhada ta nunawa Anti Bebi asirin da akayi mata domin ta kamu da son Awaisu ya kamata. A bangaren Gimbi kuma tana nan tana cigaba da wulakanta Maamu._ Ladabin karya da biyayya Shuhada ta cigaba da nunawa Anti Bebi. Ita kuma dadi ya isheta ta sami hanyar ganin hawayen Gimbi cikin ruwan sanyi. Bayan kusan sati biyu tana sanya ido akan Shuhada wadda ta dage sosai wurin nuna ita idan ba Awaisu ba yanzu sai rijiya. Hakan yasa Anti Bebi fara tunanin hanyar da zata bi domin ganin sun hadu ta fara aiwatar da kudirinta. ****** Kiran sallar magriba akeyi Rumana ta shigo gida da sauri rike da ledar kosai. Kitchen ta wuce inda take jin muryar Gimbi tana tashi taje ta mika mata ledar. Gimbi ta karba ta bude hade da zaro idanu ita ta ga abin mamaki. "Yanzu wannan kosan dari ne? Lallai wake ya soma arha. Wannan kosan ya yiwa Maamu yawa ai. Cikin tsofaffi sai ana sa ido sosai" Plate din roba ta dauko ta debi kosai guda bakwai 'yan miri-miri ta mikawa Rumana. "Maza ga kunu ki dauka ki kai mata an sha ruwa tun kina hanya." Rumana ta kalli dan siririn kofin da ko cika baiyi ba da plate din kosan sai ji tayi hawaye na barazanar kwace mata. Wai yanzu wannan ne abincin shan ruwan Maamu a gidan danta. Gimbi na kallon yadda yanayinta ya chanja a ranta tace mayu masu zuciyar kare. Zaman gidan sai kace dole sunki tafiya. Haka Rumana ta tafi dakinsu ta ajiyewa Maamu abincin shan ruwanta wanda yasa idanunta kawo ruwa itama. Kunun kansa bai wuce kurba hudu zuwa biyar ba kwarara bare kuma kosan. Rashin wadatuwa da abinci ya sanya Maamu azumin dole kusan kullum yanzu shi take yi. Abincin da aka basu rana da dare sai su hada su ci lokacin shan ruwan don su fi koshi. Wani lokacin Rumana tana yi itama. Yau kamar gaske ganin idon Awaisu da safe Gimbi tace zata yi mata kayan buda baki. A yadda ta nuna kamar ranar Maamu ta fara azumin shi kuwa ya fita yana kara jin babu macen kirki sama da matarsa. Maamu na kallo Rumana ta shige bandaki taci kukanta na tsantsan bakinciki da nadamar zuwa Abuja. Da ta fito wayar Maamun ta dauka tana shashshekar kuka ta kirawo babanta. Da yake wayar ba'a ji sai an sakata a speaker Maamu tana jin muryarsa ta karbe wayar daga hannun Rumana kafin ta tona asiri. "Harisu" Dadi yaji na samun kira daga garesu saboda kwana biyu idan ya kira ta wayar Awaisu baya rasa uzurin da zai fake dashi a matsayin dalilin rashin bata waya su gaisa. Ita kanta muryarta raunana tayi da taji yace "Maamuna" "Harisu yaushe zaka zo ka kaini Fika? Kewar mutanen gida nake yi sosai. Ina Baaba da sauran mutan gidan?" Dadi yaji domin suma suna kewarta yace "Zanyi magana da Awaisu sai ku taho idan anyiwa su Rumana hutu. Ko nazo da kaina mu taho tare" Za tayi magana ya katseta ta hanyar yi mata tambayoyi akan lafiyarta da kuma kula da cin abinci akan lokaci. "Bana so ki sake kwanciya kamar wancan karon" A ranta tunani take yi idan ba a yi saurin mayar da ita cikin dangi ba kila gawarta za a kai Fika. Bayan duk sun gaisa da 'yan uwa domin Harisun kashewa yayi ya sake kiransu Maamu rokon Rumana tayi akan ta rufawa kawunta asiri har Allah Ya kawo karshen zamansu a gidan. Ita dai Rumana ko magana ta kasa yi saboda bacin rai. Maamu na gama magana ta fice daga dakin ta nufi kitchen. A yau dole ta dauki shawarar Yusra ko don ta huce takaici. Inda ake ajiye kayan kadi na miya ta bude ta debo karkashi ta zuba a kofi wanda rabinsa ruwa ne. Tana juyawa da yatsanta bata sani ba ashe Daula ta ganta. Dakin Awaisu ta nufa inda suke hira da Gimbi ta fada musu ga Rumana tana kwaba milo da ruwa zata sha. Da sauri Gimbi ta tashi tana kallon Awaisu. "Kana ji dai da kunnenka yarinyar nan ta fara sata duk irin kokarin da nake yi akansu ita da Maamu" "Ki kyaleni da ita zanyi mata magana" shi tashin hankali ne baya so musamman da yake ya kwaso gajiya. Bata saurare shi ba ta bi bayan Daula. Yau sai ta koyawa Rumana hankali kila da safe ta bar mata gidanta. A bakin kofa suka hadu Rumana zata je dakin Gimbi ta juye kwabin karkashin a bakin kofarta. Ba karamin tsorata tayi ba da suka hada ido da Gimbi. Kofin ta fizge tayi wurgi dashi abin ciki ya watse don ma na roba ne. Sannan ta kwashe Rumana da mari. "Barauniya kawai kwadayayyiya. Wato dama kece kike karar min da madara da milo ban sani ba" Rike kumatu tayi tana kukan sharrin da akayi mata sai ga Daula ta yo kan Gimbi santsin karkashin da ta taka ya kwasheta tana neman faduwa. Garin haka bata kula ba tana kokarin rike 'yarta itama ta taka suka yi sulu a kan tiles duk su biyun suna ihu. Daula tsoron faduwa yasa ta damki kan Gimbi wanda aka yiwa kananun kitson barebari. Jela ukun da ta damko tana ja yasa Gimbi sanya wata muguwar kara, hakan yayi daidai da cizgewar kitson sai gasu a hannun Daula. Su duka biyun suka fadi a kasa jikinsu dame da karkashi. Rumana kuwa me zatayi banda dariya. Kana kallon kan Gimbi sai kayi dariyar yadda ya kwashe. Sai fada take yiwa Daula. Da kyar suka iya tashi santsi na kara dibarsu. Sai da Rumana ta ji tahowar Awaisu yana tambayar ihun me akeyi ne ta durkusa ta rike ciki. Duk da bukata ta biya amma tsoron hukuncin da zaiyi mata take yi. "Me ya sameku haka, ku duk kun zube a kasa ke kuma kina rike ciki" "Abba faduwa mukayi da wannan abin da Rumana ta hada" cewar Daula Taimakawa Gimbi yayi ta tashi amma kafarta kamar bazata iya daukanta ba don buguwa. Runtse ido kawai take yi ta kalli Rumana "Uban mene kika hada a kofin nan" Fuska Rumana ta kwabe ita abar tausayi "Cikina ne yake ciwo tun a makaranta shine wata tace min ana jika karkashi da kanwa" "Karkashi da kanwa kuma Rumana? Baki da lafiyar bazaki fada min ba sai ki hada wani karkashi" Awaisu yana magana yana kallon Daula mai kawo rahoto. "Na zata fa milo ne" ta fada kai a kasa. Dama ita ce mai zuwa hada milo da madara ta sha duk dare. Lokacin da ta ga Rumana ma abin da ya kawota kenan. Baice komai ba ya tallabo Gimbi suka tafi daki ciwo a kafarta ta hagu ya isheta. Daula sai harara take dokawa Rumana ta tafi dakinta. Ita kuwa da murna ta tafi harda danewa jikin Maamu. Bacin ranta duk ya kau saboda dadin da take ji a lokacin. Maamu bata san me yake faruwa ba amma canjin yanayin da ta gani wurin Rumana ya dan kwantar mata da hankali. ***** Daren nan Gimbi batayi baccin kirki ba saboda ciwon kafa ga kanta yana zugi. Gari na wayewa kafar ta kumbura suntum daga wurin gwiwa. Awaisu da kansa ya tashi Rumana tayi abincin safe zai kai Gimbi asibiti. Ta dan ji faduwar gaba ko a dalilinta wani abu ya sami Gimbin. Amma da ta tuna gasuwarsu a gidan sai ta share. Da kyar ya taimaka mata suka fita waje tana jan kafar. Kwakkwaran motsi idan tayi sai taji kamar ana soka mata wuka. Bayan fitarsu Rumana ta shiga fadar Gimbiya matar Awaisu inda ake horasu ta dafa shayi ta soya kwai ta zubawa su Daula nasu ta hada mai yawa a flask ta kaiwa Maamu. Ga kwai ga bread. "Rumana wannan daga ina?" "Allah ne Ya bamu Maamu. Kiyi sauri ki ci kafin su dawo daga asibitin" Dan fito da ido tayi "waye babu lafiya?" Rumana tana dariya ta labarta mata yadda sukayi jiya. Maamu ta soma yi mata fada akan kada ta kara. Amma Rumana ta kula fadan bai kai zuci ba don har dan murmushi tayi. Ranar sun ci sun koshi suna gamawa taje ta dora na rana da wuri kafin goma ta gama ta sake zuba musu mai yawa. Sai da ta koma gyara kitchen Awaisu ya dawo ya sanar dasu an kwantar da Gimbi a asibiti kashinta ne ya goce ga buguwa kafar tayi tsami. Haka nan yaji yana son ganin Maamu bayan kusan sati ko hanyar dakin baije ba. Yana shiga ta fito daga wanka. Ji yayi jikinsa duk yayi sanyi saboda wata muguwar rama da Maamu tayi. Hankalinsa yayi mugun tashi yace "Maamu baki da lafiya ne?" So take tayi kuka sai ta dake "Ka kaini Fika" Muryarta ma ta kankance kamar yadda ta rame. Duk yaji ya tsani kansa da rashin kulawa da ita. "Kiyi hakuri a dan kwana biyu ki kara warkewa sai na kaiki. Amma a haka kowa ya ganki yasan baki da lafiya" Daga murya tayi ta soma fada "Ubanka ne ya samin ciwon da zaka ce bani da lafiya? Ka mayar dani inda ka dauko ni tunda ka gagara kula dani da yar amana Rumana" Jin kansa yake kamar wanda ya tashi daga bacci a lokacin. Me ya faru tun tafiyar su Baaba ya dena bibiyar halin da Maamu ke ciki bayan yasan yadda Gimbi take wulakanta masa dangi . Kamar wani yaro ya soma hawaye a gaban Maamu amma ya rasa me zaice mata. Tausayinsa ya kamata itama sai kukan. [15/08, 17:45] ‪+234 803 272 5896‬: *KASHE FITILA*💡 24 *Batul Mamman*💖 Sai da suka yi mai isarsu sannan tace ya tashi ya fita bata son ganinsa. Jiki a sabule ya fita ransa yana kuna. Mamakin kansa yake yi da yadda yake sakaci da mahaifiyarsa. Shi Awaisu manajan banki kuma babban dan kasuwa shine Maamunsa take wadannan kasusuwan kamar wadda ta shekara ciwo. Tun shigarsa daki tunani kawai yake yi karshe bacci mai nauyi ya dauke shi. A asibiti sai shabiyu likitan kashi yazo aka gyara kafar Gimbi. Tasha azaba gumi ya rinka bin jikinta saboda ciwo. Ga kanta inda Daula ta tsige mata kitso ya tashi sosai kafar gashin da ya fita ta kumburo shima ciwon yake mata. Duk wannan ya taru da rashin dawowar Awaisu daga cewa zaije gida ya dawo. Tayi ta kiran wayarsa shiru baya dauka. Nan fa ta damu sosai ta fara tsoron ko aikin Wangesi ya soma rabuwa dashi ne yau daya da batayi masa turare ba. Abu kamar wasa har azahar bai dawo ba kuma babu waya. Ganin haka hankalinta duk ya tashi har ta fi damuwa da rashin dawowarsa akan ciwon da jikinta yake yi. Takurawa wata likita tayi akan lallai sai an sallameta suka ki. Da ta rasa abin yi sai ta kira Anti Bebi. "Gimbiya ta Awaisu yaya akayi ne?" ta fada tana dariya Gimbi ta amsa mata da kyar ta labarta mata halin da take ciki. Kamar gaske Anti Bebi ta nuna damuwarta ta shirya ta taho asibitin. Da tambaya ta gane dakin ta shiga. Tana budewa ta ga kan Gimbi sai dariya har ta kusa kaiwa kasa. "Gimbiya wannan kyan ki hoto wallahi a kafa shi a kofar gidan Awaisu." Daure fuska Gimbi tayi "wannan ciwon fa ba na wasa bane Anti Bebi" Da gayya ta kaiwa kafar da aka nade duka cikin wasa ita kuwa Gimbi ta saki kara har tana jin fitsari na barazanar fita saboda azaba. Anti Bebi ta dauke kai kamar bata kula ba "nima ban ce na wasa bane, wai.... wannan kai naki kamar na budurwar zabuwa a lokacin da ta fara kora. Awaisu ya caba da Gimbiyar mata" Ran Gimbi in yayi dubu ya baci har ta fara dana sanin kiranta. "Idan dariya zakiyi min ki tafi kawai na nemi taimakon wani" "Dadina dake tsiwar tsiya. Me kike so dai yanzu" Tunanin yadda zatayi maganin Gimbi a nan gaba take yi. Dauriya ce kawai yanzu take kafin lokacin da zatayi dariya. "Saboda wannan ciwon yau banyiwa Abban Haris turaren nan ba. Kinga tun fitarsa har yanzu shiru. Ina tsoron kada hankalinsa ya fara komawa kan uwarsa" Anti Bebi ta murmusa "Gimbi Allah dai Ya baki suruka irinki. Nasan ba karamin dadi zaki ji ba ke me 'yan maza har uku su auri mata masu jajircewa akan mazansu kamar ki" Gimbi ta dafe kirji jin wannan muguwar addua daga bakin Anti Bebi. "Ba Amin ba wallahi, wai me nayi miki ne haka kike min mugun baki?" "Auuuuu, ashe babu dadi kike yiwa Maamu baiwar Allah? To maida wukar wasa nake yi. Amma ni kam gaskiya da ina da da namiji wallahi bazan bari ya aureki ba." Ganin cewa cin fuska Anti Bebin take yi mata tace ta tafi kawai ta fasa. Anti Bebi taji dadi ga dama ta samu na hada Shuhada da Awaisu tace tayi hakuri. Kwantar da kai sosai tayi tana bata baki Gimbi na hura hanci ita a dole ta isa. Bayan sun gama magana akan cewa Anti Bebi za ta je har gidan da sunan dauko mata kaya tayi masa turare ta dauki jakarta. "Ki jirani da kansa zai zo har nan ya sameki ki sille shi ciki da waje." ****** Gidanta ta wuce kai tsaye tana murmushi. Da yake ita ke tukin motar ko yaya ta tuna irin mugun tanadin da ta yiwa Gimbi sai ta daki sitiyari tana dariya. Da isarta Shuhada ta umarta da ta shirya zasu fita. Ita kanta wanka ta sake yi tamkar kanta zata kaiwa Awaisu ta saka riga da zani na mutumci harda hijabi. Shuhada ma doguwar riga ta saka mai kyau yalwatacciya da hijab wanda ya wuce kirjinta da kadan. Ganin shigar da Anti Bebi tayi abin ya daure mata kai sosai tuni ta sha jinin jikinta. Dole ta san yadda zata gabatar da kanta ko ma ina zasu je don kada asirinta ya tonu. Wayar da tayi da mamanta da safe ta tuna inda ta nuna tafi son 'yarta ta dawo gabanta ita kuma tayi ta lallabata akan ta kara hakuri na dan lokaci. Ajiyar zuciya tayi ta bi bayan Anti Bebi. Kasuwa ta biya ta sayi kaji manya manya guda shida danyu sai kayan marmari. Daga nan suka wuce gidan Awaisu. Yana kwance a daki har lokacin sallar azahar da ya makara a gida yayi. Rumana ko tunanin ta zuba masa abinci bata yi ba. Girki dai tayi yau a koshe suke a ranta a shirye take da duk hukuncin da Gimbi zata yi mata idan ta dawo. Har ayyanawa take idan ma dukanta tayi itama ramawa zatayi sai dai yau a korata gida kamar yadda take so. Kamar daga sama taji dirar mota. Haba a take jikin Rumana ya dau mazari tayi zaton Gimbi ce. Yau tasan mai rabasu sai Allah yadda tayi barna a kitchen. Maamu kanta da ta ga naman da ta zuba mata a miya sai da tayi mata fada akan tayi wauta. Tashi tayi daga falo zata gudu daki neman ceto a wurin Maamu taji muryar Anti Bebi da wata siririyar murya suna sallama. Su Haris ne suka fito tarbarta. Rumana tana rarraba idanu taso ta ganeta amma da yake ba haduwa suke yi sosai ba ta manta inda suka hadu. Anti Bebi na ganinta ta ware hannu ta tafi da sauri ta rungumeta. "Rumanan Maamu ina Maamunki?" Rumana tayi sakato tana duban su daya bayan daya. Dafa ta Anti Bebi tayi "Baki ganeni ba ko, Auntyn Mummyn su Haris ce. Ina Maamu kaini na fara gaisheta kafin na nemi 'yata" Hannun Amir ta ja tana masa hira wai ina mamansu take ne ko don yau lahadi tana can tana bacci. Har kasa ta kai gwiwarta ta gaishe da Maamu. Itama Shuhada gaisheta tayi tana tausayin rayuwar dattijuwa da aka asircewa da ya kama ta. Waige Anti Bebi ta soma yi tana neman Gimbi. Daula ta sanar da ita tana asibiti tun safe. Mamaki ta nuna tare da dafe kirji "Me ya sameta haka?" Yaran kusan a tare suke bata labarin hatsarin Gimbi da ruwan karkashi. A haka Awaisu yazo ya samesu ya fito sanye da shirt da wando da gani wanka ya sake. Ganin Anti Bebi ya sanya shi sake hade fuska ita kuwa ta dan taba Shuhada wadda tayi saurin gaishe shi tana binsa da kallo wanda a zahiri mutum kamar Anti Bebi zaiyi zaton na soyayya ne. Murmushi Anti Bebi tayi tana nuna Shuhada "Ka ganta nan ita ta hanani sakat wai zata zo gaishe da Maamu. Tun zuwanmu asibiti dubata take sonta." Kafe Shuhada tayi da ido ita kuma tayi saurin kallonsa tana rausayar da kai tare da murmushi. "Don fitina kaji tasa muka saya wai a nan zata dafa mata irin yadda take so. Yini taso yi ni kuma bana jindadi gashi yau dreba yana hutu dole na daure muka fito" ta kare zancen da fara'a kamar yau take sallah. Maamu dai kallonsu take yi bata ce komai ba har Anti Bebi tace da Rumana su tafi kitchen da Shuhada su gyara naman kada ya lalace. Da ido Awaisu ya bi bayan Shuhada da kallo ya kasa gane me zuciyarsa take ji a lokacin. Suna fita Anti Bebi ta zauna a kasa kusa da Maamu. "Maamu don Allah ki rinka hakuri da 'yar tawa. Nasan zama tare da sukuka sai an daure anyi hakuri. Dan yanzu ka haifeshi ne baka haifi halinsa ba" Tana magana tana rike da hannun Maamu wanda take ta mammatsawa a hankali kamar mai tausa. Maamu ta dago suka hada ido a take taji wani irin firgici ya ziyarceta. A yadda zuciyarta ke rawa bata jin akwai wani abu da Anti Bebi zata nema a gareta ta gagara yi mata. Wani murmushin gefen baki Anti Bebi ta sake yi tana kara murzawa Maamu sauran maikon maganin da Wangesi ya bata na mallake mata zuciya. Awaisu da ke tsaye yace da Maamu zaije asibiti idan an gama su dawo. Fada ta soma yi masa na rashin komawa bare ayi batun abinci. Rumana ta kwalawa kira taje ta hada abinci ya tafi dashi. Anti Bebi taji suna yaren da bata ganewa ta tashi wai itama asibitin zata je amma zata bar Shuhada idan ta dawo su tafi tare. "Maamu bari na bishi na gano jikin nata" Ba don yaso ba suka tafi tare tana ta yi masa hira duk ta ishe shi. Abincin ma ita ta dauka ta shiga dashi dakin. A kwance Gimbi take suka shigo tayi saurin tashi zaune. A zatonta an gama yi masa turare ne Anti Bebi ta sako shi a gaba suka taho. "Ni zaka yiwa haka Abban Haris? ka kawoni asibiti don wulakaci tun safe babu ci babu sha sannan ka ki dawowa. Ina ma ka shiga tun dazu ina ta kiran wayarka ka ki dagawa." Bata jira amsarsa ba ta cigaba da cewa "akan wannan me billen daga goshi har kan hanci zan huce. Bari na koma gida sai sun gane kurensu" Zuciyar Awaisu ce take masa wani irin tafasa yana tunanin ko dai Gimbi ta sha kwaya ne ko kuma kitson da aka tsige mata ya taba mata kwakwalwa. Anti Bebi kuwa ta lumshe ido tana jin cewa lallai hakanta zai cimma ruwa indai Gimbi ta cigaba da hawa dokin zuciya tana sakin layi a tunanin asiri ke aiki. [15/08, 17:45] ‪+234 803 272 5896‬: *KASHE FITILA*💡 25 *Batul Mamman*💖 Abubuwa da dama ya rinka tunawa a lokacin wandan da suka gabata. Kamar yadda ya dauke kai daga mahaifiyarsa da kuma wasu abubuwan da Gimbi take saka shi yana yi babu ko tambaya. Ba tare da cewa komai ba ya juya ya fita tana ta kwala masa kira. Tana ganin fitarsa ta fara kokarin tashi a tsorace Anti Bebi ta daga mata hannu alamun ta zauna. Fita tayi ta bi bayansa ita kuma Gimbi duk ta gigice tana neman yadda zatayi ta sauko daga kan gadon ta bi bayansa. Mugun saurin da yake yi yasa Anti Bebi sai da ta danyi gudu ta iya taddo shi. "Awaisu dakata don Allah" A fusace ya waigo Anti Bebi ta fashe da kuka irin mai tsuma zuciyar nan ta dago kai tana kallonsa. " Ashe haka kake fama dan nan? kayi hakuri ka ji Awaisu." Wani kallo shekeke ya bita dashi sannan ya juya ya shige motarsa ya buga kofar da karfi ya fita daga harabar asibitin a guje. Me Gimbi ta dauke shi ne? Har yaushe raini ya shiga tsakaninsu irin haka? Sannan garin yaya ya sakar mata ragamar gidansa har ta kai zata iya kiran mahaifiyarsa mai bille? Yau ba don a gadon asibiti take ba yana jin babu wani abu da zai hanashi yi mata duka a wurin. Kafin ya karasa gida zuciyarsa ta cika da tsanar kansa da dana sanin auren Gimbi. ***** "Mai babbar kujera Wangesi na kan tudu na yarda na amince idan ina da kai duk wata matsalata ta kau" Yayi wata dariya mai sautin kukan rikakken alade daga inda yake kwance wata mata wadda akalla zata kai shekaru hamsin da biyar tana yi masa tausa. A kowane hannun matar yatsu uku sanye suke da zobba na gwal manya. Leshin jikinta mai matukar tsada da kyau. Fatar jikinta kadai ta isa ta nuna arzikinta. Hannu ya daga yana yi mata nuni ta dakata haka sannan ya cigaba da waya da Anti Bebi. "Idan kina shakku a da yanzu nasan kin tabbata aljanu na sun tsaya min. Kamar yadda suka yi alkawarin tayar da rikici tsakanin Gimbiya da mijinta kin gani da idanunki" Jinta take kamar ta zuba ruwa a kasa ta sha tayi dariya "na yarda Wangesi na kan tudu. Aikinka yayi kyau sai nazo" Kusan tare suka ajiye wayar ya dubi matar da take zaune a gefensa. "Kin gama komai ne?" Ta dukar da kai a ladabce "na gama Wangesi" Dakin nasa ya karewa kallo. Ta share ko'ina tas ta goge. Daga gefe inda bandakinsa yake ta wanke shi har ana jin kamshin turaren da ta saka a dakin. Lokacin da ta shiga wani uban zarni da wari yake haka ta rinka amai kamar zata fitar da kayan cikinta. Bayan ta gama ta wanke masa kayansa su ma doyi suke yi babu kyaun gani. Ga kuma girki wanda ita da kanta yasa tayi masa cefane ta dafa masa shinkafa da miyar kaji. "To Hajiya Dela kinyi duk abin da Aljani Sukku ya bukata. Yace kije sa'a dai a wannan kasuwancin da zaki fara ko tsinke kika daga zaki sami mai saya." Murmushi tayi tana kada idanu kamar yarinya. "Nagode Wangesi, yadda kuke bani sa'a akan dukkan abin da nasa a gaba dole nayi biyayya." Wani dan kulli ya miko mata. "Wannan ki samu ki jika su tsumu na kwana uku sai ki hada lemo dashi ki bawa shi maigidan naki. Ina mai tabbatar miki ko nawa kika bukata jarin zuwa Dubai din zai baki kuma bazai taba saka miki ido wurin shige da ficenki ba" Kullin ta bude inda ya zuba faratansa na hannu da kafa zako-zako masu matukar dauda wanda ta yanke masa kafin ta fara aikace-aikacen da ya saka ta. Godiya sosai tayi masa ta tashi ta fita tana tofar da yawu saboda warin da take ji yana fita daga jikinta. ****** Anti Bebi ta koma dakin Gimbi inda ta sameta tana ta kokarin sauko da kafarta wadda aka gyara ta kasa. Saurin zuwa tayi tana gyara mata kafar "Haba Gimbiya ina zaki je haka da wannan kafar" "Ki kyaleni naje Anti Bebi, ko dai kinyi kuskure a turaren ne?" Gwalo tayi daga bayanta sannan ta karya murya kamar gaske " kada ki daga hankali akan wannan. A yau zanje Wurin Wangesi sai na ga abin da Awaisu yake takama dashi. Kada ki bari komai ya daga miki hankali. Gimbiya ko babu mai tsaya miki duk duniyarnan bazan taba bari ki wulakanta ba". Da kalamai masu dadi da kwantar da hankali Anti Bebi ta cigaba da hillatar Gimbi har ta sami nutsuwa. Abu na karshe da ta fada mata shine ta dena yarda da zancen Wangesi shi kadai. "A matsayinki na mace ban da asiri dole ki hada da kissa. Shigowarsa dazu maimakon ki nuna kinyi kewar rashinsa sai kika saki baki kina diga rashin mutumci. Yayi miki da sauki ma. Nice shi sai na daukeki da mari kafin na fita" Idanu Gimbi ta ware tana kallon Anti Bebi kafin ta girgiza kai tace "Lokuta da dama sai na rinka jin kamar ba kya kaunata. Yanzu banda kin kware a mugunta da keta meye na cewa da kece sai kin mareni?" "Fitsarar ce ta tashi daga yi miki gyara?" "Admit it Anti Bebi my misery gives you pleasure" Da yake duk gayu da mugun halin Anti Bebi babu boko don ko sakandire bata gama ba kasa amsawa tayi sai tsaki da ta buga tare da surar jakarta. Gimbi tayi dan murmushi "Uwata ta kaina tuba nake yi. Idan kika barni yanzu karshenta aurena ya mutu" Ita ta dawo shawo kan Anti Bebin suka cigaba da musayar bakaken kalamai kafin su daidaita. ***** Kafin Awaisu ya karasa gida yamma tayi sosai. Yana tsayar da mota su Amir suka tarbe shi da cigiyar Mummynsu. Shafa kawunansu kawai yake rai a bace ya kasa basu amsa. Falo suka shiga yana sauri ya wuce dakinsa ya kwanta ko zaiji saukin radadin maganganun Gimbi yaji wani kamshi ya doki hancinsa. Bai gama tantance ko na meye ba Shuhada da Rumana suka fito kowacce dauke da tray din abinci. Ai yana ganin Shuhada ransa ya kara baki ya daka wata tsawa da ta tsorata duka yaran da Rumana har hannunta na rawa zatayi bari. Da kyar ta saita kanta suka taru suna kallonsa. Fuskarsa kamar bai taba dariya ba ya harari Shuhada "zo ki fice daga gidan nan yanzun nan" Duk da ta tsorata sosai dakewa tayi ta tsaya a wurin. Ba wani abu take nema daga Awaisu ba face ya bata lokaci ko yaya ne tayi masa bayanin matarsa da kanwar babarta. Uwa uba idan ya nuna kyamarta da wuri yadda Anti Bebi tayi imani da asiri tana iya ganewa karya tayi mata. Daga nan kuma bata san hukuncin da zata yanke mata ba. Neman abin fada ta fara Maamu da ta shiga falon a lokacin ta katseta. "Menene hakan da kake shirin yi? Ka gama wulakanta ni son ranka yanzu Allah Ya kawo mai tausayina za ka koreta. Tun da kuka fita take yi min hidima kamar 'yata ba kamar matarka ba" Kallonsu Shuhada tayi tana mamaki ashe ba Hausawa bane. Shima cikin yarensu ya bata hakuri sannan dubi Shuhada "Ana yin sallah ki fito ki tafi ita wadda kuka zo taren tana asibiti." Bata nuna masa bacin rai ba sai ma marairaicewa da tayi a gaban Maamu. "Gashi ban iya mota ba kuma bata bar min mukulli ba. Maamu bari na ajiye miki wannan sai na tafi tun yanzu kafin magariba ta karasa na rasa abin hawa" Maamu tayi murmushi "A'a 'yata ki bari ayi sallah zai kaiki har gida. Nagode miki sosai" Bai iya cewa komai ba ya wuce. Duk mutum mai alaka da Gimbi haushinsa yake ji. Yana idar da sallah ya bukaci tazo su tafi. Maamu tayi ta sa mata albarka suka yi sallama da Rumana. Motarsa ya nuna mata ta shiga ita kuwa ganin su Rumana sun koma ciki ta dago ido tana masa kallon da yasan ko me zata fada babu wasa a ciki. "Ina son muyi magana da kai ne." Ya dan matso inda take domin jin abin da take son fada suka ji alamun an rufe gate. [15/08, 17:45] ‪+234 803 272 5896‬: *KASHE FITILA* 💡27 *Batul Mamman*💖 _Taqabbalallahu Minna Wa Minkum_👏🏽 Wani irin numfashi Anti Bebi ta rinka saukarwa mai kama da gurnani. Bata san tsahon lokacin da dauka a haka ba sai ji tayi ana kwankwasa glass din motar ta saitin inda take. A firgice ta bude ido ta saukesu kan wasu jajayen idanu manya. Tafiya tayi luuuu zata sake suma taji ance "baiwar Allah lafiya kike?" Mace ta gani a kusa da mai jajayen idanun taji hankalinta ya kwanta. Da sauri ta bude ta fito. Sai a lokacin ta kula mutane sun kai biyar da suka zagaye motar ana tunanin ko wani abu ne ya sameta. Karyar ciwo tayi musu ta kulle motar ta nemi tasi ta shiga. A cikin motar ma duk da shata tayi ta zauna a baya amma haka taji duk an matseta. A takure ta isa gida babu damar magana don shi kanshi dreban motar tsoronsa take yi. ****** Da shigar Anti Bebi gida ta soma kiran Wangesi baya dauka. A yadda take jin jikinta kamar ana daureta dole ta tafi wurinsa neman taimako. Drebanta ta kira bata la'akari da yamma ta kawo kai tace su tafi kan tudu wurin Wangesi. Sun isa farko-farkon magriba. Jikinta duk ciwo yake mata saboda wata irin matsuwa da tayi a bayan motar. Gashi dai ita kadaice amma kamar su biyar ko shida take jin sun zauna a takure. Tsabar sauri kafarta daya babu takalmi haka ta fada cikin gidan Wangesi. Dakin da yake ganin bakinsa irinta ta shiga ko iso bata tsaya yaransa da suke masa aiki sunyi mata ba. Mata uku ta samu a wurin suna gabatar masa da matsalolinsu. Yana ganin Anti Bebi kamar an jehota daga sama ya mike tsaye "Hajiya Bebi lafiya?" Haki take yi tana maida numfashi da kyar murya a sarke tace "ina fa lafiya Wangesi yau nayi gamo" Matan da suke dakin suka fara kallon-kallo. Wangesi ya samu ta dan nutsu ta labarta masa abubuwan da suka faru da ita tun daga farko. Wani tsalle ta ga ya daka ya daga hannuwa sama "Ehooooooo, Ehooo. Waye yace dani bani ba? Sai ni nan uban kan tudu mai aiki da hatsabiban aljanu" Juyi yake yi yana furzar da yawu ransa yayi matukar baci. Can ya fita ya dawo da wata tukunyar kasa sai wari take yi. "Bebi tun farkon zuwanki wurina sama da shekara goma me na fada miki?" A daburce ta tambayeshi "meye hadin farkon zuwana da wannan masifar da na tashi da ita?" "Bari na tuna miki idan kin manta. Aljanin da yake miki aiki baya son kishiya kuma na sanar dake duk ranar da kika je wurin wani bokan yace a bata duk wani sihiri da aka taba yi miki. Sannan ki jira abin da zai biyo baya. Na tabbata wurin wani kika je shiyasa haka ta faru" Idanu ta zaro kamar su zube a kasa "ni kuwa me zai kaini wurin wani ina da kai....na rantse maka da....." Tusssss taji kafin ta gama rantsuwar ya saki tukunyar da take kunshe da dukkan wani asiri da ya taba yi mata. "Aljanin bashi da hakuri ko kadan Bebi. Ki fita daga gidan nan kafin yazo mu duka mu fuskanci bacin ransa." Matan nan uku na jin haka suka runtuma a guje. Anti Bebi kuwa a gaban tukunyar ta durkusa tana wanj gunjin kuka "Wangesi ka tona min asiri. Cikin kasa da awa biyar duniya tayi min juyi irin wannan? Na shiga uku...." Kara murtuke fuska yayi "ke kika janyowa kanki ko ma menene. Ki fice min daga gida kafin ya iso gareki" Jikinta sam babu kwari ta mike tsaye da kyar. Zuciyarta ke fada mata ko dai mafarki take yi duk wannan bala'in ba gaske bane. Da jan kafa ta fita waje. Tana sa kafa a wajen taji an rungumeta tsam ana yi mata magana a kunne har tsigar jikinta na tashi "Oyoyo Bebi, kika barni ina ta jiranki a nan. Zo mu tafi na fara jin yunwa" Drebanta yana cikin mota ya hangota ta fadi a sume ya fito a guje ya fara neman yadda zai sakata a mota. ***** Maamu ta gama cin tuwo kenan Baabu Hure ta shigo dakin suka fara hira. Cikin hirar Baaba ta sako zancen auren Awaisu da yake ta matsowa "Yanzu Maamu kina ganin babu matsala wannan auren na yaron nan? Kin dage sai anyi auren nan ba kya tunanin kada matsala ta taso ganin akwai alaka tsakaninta da Gimbiya" Hannun Baaba ta kama ta rike tana magana a hankali "Baaba Hure ina ganin a bar maganar auren nan kawai. Ni bansan me ya kaini tunanin hadasu ba " Baki Baaba ta saki tsabar mamaki ya cikata. Maamu da har kusan kuka take yi akan anki gaggauta auren shine zata ce ta fasa. Anya mutanen nan haka suka barta kuwa? Katse mata tunani tayi da muemushin da yafi kuka ciwo "yarinyar nan Gimbi nake so ayi masa bikonta. Ita kuma waccan sai a basu hakuri. Ba kiji yadda raina ke suya ba idan na tuna uwardakinta Bebi dinnan. Matar tsoro take bani." Baaba kasa magana tayi don abin yafi karfin mamaki. Maamu sai magana take yi mara kan gado. Karshe ta kwanta ta juyawa Baaba baya. Tashi Baaban tayi zata fita taji sheshshkar kukan Maamu. Fita tayi tana share kwalla. Ta rasa mene ne yake damun Maamu da har take kuka amma ta kasa fadawa kowa damuwarta. ***** Daren ranar Anti Bebi tamkar tayu hauka. Dadinta ma Alh Maitama yayi tafiya. Shuhada kuma ganin yadda ta shigo musu a birkice ko ta kanta bata bi ba. A bangaren Gimbi tun da ta koma gida ta kasa nutsuwa. Zuwa yanzu yaci ace aikin bokan Ovi ya fara kamawa. Idan taji shiru har safiya tasan akwai matsala dole ta canja salo. Wurin shadayan dare wayarta tayi kara alamun text ya shigo. Tayi zaton kamfanin layin wayarta ne ta share. Sai dayan dare ta dauki wayar zata duba lokaci ta ga sakonni sumfi hamsin daga Awaisu wanda mugun son Gimbi yayi masa kawanya a zuciya. Murmushi tayi ta duba na farkon (Na mayar dake Gimbiyata ki dawo gareni Na biyun kuma (Ki bani izinin kiranki a waya) Haka tayi ta bin sakonnin tana karantawa a tsaye don zama ya gagareta. Murna take yi mara misaltuwa. A daren ta hada kayayakinta ko runtsawa ta kasa yi. Kafin takwas na safe ta turo akwatunanta falo tana kiran maigadi yazo ya kai mata mota. Hayaniyarta ce tasa Mama fitowa ta ganta a shirye zata fita. "Ina zuwa da sanyin safiyar nan?" Fuskarta na nuni da tsananin farinciki ko gaishe da Maman bata yi ba ta mika mata wayarta "Gida zan tafi Abban Haris ya mayar dani" Marinta Mama tayi niyar yi sai ta fasa ta samu wuri ta zauna a sanyaye "Gimbi a tunaninki abubuwan nan da kike yi kin dauko hanya mai billewa kenan? Da ban fito ba sai dai mu nemeki mu rasa kenan ko. Hmm bazanyi miki baki ba amma ina mai baki shawara ki kiyayi duniya. Komai nisan jifa kasa zai fado, komai nisan dare gari zai waye...karshe kuma ki sani abin da ka shuka shi zaka girbe." Kallon Mama tayi na dan lokaci sai kuma ta figi karamin akwatinta tayi gaba tana cewa ta gaishe da Babanta idan ya tashi. Tana fita Mama ta fashe da kuka tana yiwa Anti Bebi Allah Ya isa. ****** Cikin bacci yake ta buge buge batare da ya sani ba. Kana ganinsa kasan duk yadda akayi mugun mafarki yake yi. Mutanen kusa dashi suka fara juyowa ana kallonsa. Hakan yasa abokinsa da suke tare Kamilu ya soma girgiza shi. "Kai T a train muke fa. Meye haka?" Tajuddeen ya bude idanunsa da suka masa nauyi a hankali. Hannun Kamilu ya damko tamkar wanda zai gudu ya barshi. "Kamilu meyasa na saki S?" Harara Kamilu ya jefa masa sannan ya fizge hannunsa "Dalla malam cikani" Tajuddeen ya sake rike masa hannu "wallahi Kamilu da gaske nake. Haka kawai fa ranar na shiga gida na hauta da fada mara dalili sannan na saketa" Kamilu sake hararsa yayi sai ya kula hawaye Tajuddeen yake yi. Zuciyarsa ce ta dan karye ya dafa kafadarsa. "Wannan ba magana bace ta nan T. Ka bari mu karasa gida sai muyi a nutse. Kaga sai kallonmu ake yi" Ba don yaso ba ya hakura amma da shigarsu gidan Kamilu ko zama basu yi ba Tajuddeen ya sake tado maganar. "Wai T kayi gamo ne a train dazu? Dama wani shure shure naga kanayi cikin bacci har kasa ana kallonmu. Anyways me kake son ji game da rashin mutumcin da ka aikata" Sunkuyar da kai yayi yana tuna ranar da ya saki Shuhada da irin wulakancin da yayi mata. "Bani da wani dalili na abin da na aikata Kamilu. Haka kawai kamar wanda akayiwa asiri. Saki har uku" ya karashe hawaye na bin kuncinsa. Duk irin haushinsa da Kamilu yake ji dole ya tausaya masa. "Al'amarin nan naku da daure kai. Kasan da ka dena kiran mutanen gida akan fadan da suke maka na sakin da kayi Umma ni take nema. Kuma abin mamaki ana nake jin ashe itama Mummynsu Shuhada itama nata auren ya mutu" Tajuddeen ya dan kada kai "kasan labari mara dadi babu amfanin bayar dashi. Shiyasa ban taba fada maka ba. Baffanmu ya bani labari ba karamar soyayya bace tsakanin iyayen S. Kasan duk garinsu daya. Shiyasa muka yi mamaki sosai da yayi sakin. Tunda ya auro wata mata Bebi shikenan gidan ya rikice." "Bebi fa kace" Kamilu ya maimaita da sauri. Kai Tajuddeen ya gyada masa kawai. "Bebi dai wata doguwa siririya ko, idan tana tafiya duk jikinta sai ya motsa" Murmushin dole T yayi saboda yadda Kamilu yake kwatanta Anti Bebi "Ita ce, ka santa ne?" "Allah Masani amma ina kyautata zaton ita ce sanadiyar wannan sakin naka da na baban Shuhada. Ta taba auren wan mamanmu, cikin wata biyu sai da ya saki matansa uku da suke gidan. Dama cikon ta hudun ya saka ya aurota. A shekara dayan da sukayi tare sai da ya zare hannunsa kan duka yaransa daga shi sai Bebi poison yadda yaran suke kiranta" Lallai biri yayi kama da mutum. Dama irin labaranta da yaji daga wurin S da kuma wanda ido ya gane masa yasan zata aikata. Muguwar tsanarta ce ta kara shigarsa ya fara tunanin irin hukuncin da zaiyi mata. Kafadarsa yaji an dafa ya kalli abokinsa Kamilu "Wallahi bata ci bulus ba. Gida zan koma a cikin watan nan. Kafin nan za ka rakani wurin Suhail a makaranta" ***** Awaisu tun jiya ya kasa zaune ya kasa tsaye saboda tunanin Gimbi. Kafin gari ya waye sau uku yana kukan da ya rasa dalilinsa. Shi dai a iya saninsa da kansa ya saketa saboda baya son halayenta. Yanzu kuma ya rasa wace jarabarce tasa duk da baya son halayen nata yake jin idan bai dawo da ita ba komai zai iya faruwa dashi. Haka nan a daddafe ya jira gari ya waye ko wanka baiyi ba ya fita zuwa gidan Alh Mudi bikon matarsa. Mama da Alhajin ya tarar suka gaisa a mutumce sannan suka sanar dashi ta tafi gida. Ko sallamar kirki bai iya yi musu ba ya fice. "Amina kada fa Allah Ya kamamu da hakkin Awaisu. Kinga babban mutum ya zama wani lusari akan mace." "Alhaji na fika damuwa domin ta bangarena Gimbi ta samo wannan mugun halin. Na rasa yadda zanyi da ita" kuka ne ya kwace mata na takaicin halin 'yarta Alhaji yayi ta rarrashi da bata baki akan su dage da addua. Gida Awaisu ya wuce ya fara karo da wani mugun hayaki da Gimbi ta soma yiwa gidan. Suna hada ido ta fito rike da kasko a hannunta yaji jikinsa ya mace bashi da wani kuzari. Da fara'a ta tarbe shi suka shige daki yana binta kamar rakumi da akala. Ko awa biyu batayi da dawowa ba tace ya tura dreba a dawo mata da yaranta. Haka kuwa akayi babu musu ya tura dreban yace a dauko harda Maamu da Rumana da sassafe washegari su taho. Rumana tayu kuka har hawaye suka nemi kafe mata saboda bakincikin komawa Abuja. Maamu kuwa bata iya cewa komai ba. Haka suka shirya da safe Harisu yana ta mita suka tafi. Bayan fitarsu ya kira Awaisu ya nuna rashin jindadinsa game da hakan amma yayi masa uzuri tunda babu mata a gidan. Awaisu bai nuna masa Gimbi ta dawo ba sai da yace zasu taho biko sannan ya fada masa. Har ya ajiye wayar yana ta mamakin sauyi irin wannan daga kaninsa. ***** Anti Bebi na kwance a daki tayi zuru zuru saboda yadda aljanu suke wasan 'yartsana da ita a daki. Tana zaune zata ji ana fadan waye zaiyi mata wanka da mai taje mata kai. Gashi Alhaji ranar zai dawo. Shuhada ta leka dakin sau biyu tana ganinta a zaune ko gaban mudubi ko a kan gado shiyasa bata kawo komai a ranta. Kofa taji ana tabawa ta zabura ta tashi tana jan bargo zata rufe kanta. Alh Maitama ne ya shigo a fusace Shuhada tana biye dashi tana tambayar me ya same shi. Wurgi yayi da jakarsa da babbar riga da ya dawo dasu a hannu ya haye gadon ya finciko Anti Bebi. "Munafuka algunguma zo ki fita daga gidan nan" Tunda Wangesi ya juya mata baya dama tasan tata ta kare sai dai batayi tunanin abin zai kai haka ba. Tattaro dan karfin hali tayi harare shi "Alhaji ni kake yiwa tsawa haka" Mari ya rinka zabga mata Shuhada da take gefe ta tsorata sosai. Tana kallo babanta yayiwa Anti Bebi duka kamar bazai barta da rai ba sai da ya gama ya koma wurin 'yarsa ya rungumeta yana kuka "Shuhada kuyi hakuri na dauko muku jaraba ta wargaza mana gida. Ni yanzu Kaduna zani wurin Mummynku." Kukan farinciki take itama tace zata bishi. Cewa yayi ta shirya tana fita ya rufe kofar dakin da mukulli "Hajiya Bebi so nake duk inda takardun kadarorina suke ki dauko ki bani tun muna shaida juna. Na rantse miki ko tsinkina bazaki tsira dashi ba." Dan abin da take sa ran tsira dashi taga Alhaji zai shiga tsakani ta fara tsiwa baki bai mutu ba. Ai kuwa ta jawowa kanta sabon duka. Sai da taji kamar bazatayi rai ba ta tashi da kyar ta dauko masa wasu da suke dakin. Sauran kuwa a wani store taje ta dauko. Security yasa suka tafi da ita police station yace zaiyi waya da komishina. Burinsa a tsareta har ya dawo daga wurin uwar 'ya'yansa. Sai bayan sati uku aka maida auren iyayen Shuhada. A lokacin Anti Bebi duka accounts dinta Alh Maitama yasa an rufe ya bita da saki uku kwarara. A bangaren su Gimbi wannan dawowar su Maamu suna gasuwa sosai. Kanwar Ovi mai suna Rita ta dauko matsayin mai'aiki. Itace kuma yar aike zuwa gurin boka. A haka ne wahala tayi wahala Rumana tayi suman karya ta samu ta koma Fika gaban iyayenta. *Wasa farin girki* _ayi hkr da rashin editing_ [15/08, 17:45] ‪+234 803 272 5896‬: *KASHE FITILA*💡 28 *Batul Mamman*💖 Maman Rumana ta daga labule ta shigo daki da sallama ta tarar da Rumana tana zazzaga madarar cowbell a hannunta tana lasa. Har wani lumshe ido take yi tana kada kai duniya ta samu. Ran Mama ya baci ta kai mata duka a gadon baya. "Tun dazu nake kiranki kunnenki kamar an toshe da auduga kin kasa ji bare ki amsa" Watsi tayi da madarar ta hau sosa wurin da hannuwanta duka biyu ta soma bata hakuri. Mama ta cigaba da mita "Tun da kika dawo gidannan sai cin tsiya da kwadayi kamar 'yar yaye. Da girmanki kike wani lasar madara" Rumana ta dan murmusa "wallahi Mama protein ne yayi karanci a jikina." "Ke kika sanshi ni ban sanshi ba" "Mama wai baza'a dauko Maamu bane? Ta fini shan wahala sosai" sai kuma ga hawaye ta fara kukan rayuwar da ta baro Maamu a ciki. Sau biyu tana mafarkinta kwana biyun nan duk ta damu. Jin Maman bata ce komai ba ta dan matsa kusa da ita. "Mama don Allah ki yiwa Baba magana kada ta mutu da yunwa.." "Kada na sake jin wannan maganar a bakinki. Yanzu haka babanku zaiyi bincike kuma wallahi idan karya kika shara mana don kawai ki dawo nan kema kinsan bazata kare miki da kyau ba. Kuma zamu tattaraki ne a mayar" Zumbur ta tashi tsaye jin hakan "Mama ni da gidan Uncle Awaisu fa har abada. Kai ni ko Abuja bana fatan Allah Ya sake kaini. Mama! Mama!! idan kuka mayar dani Abuja wallahi guduwa zanyi na shiga duniy... " Bakin nata Mama tayi saurin dokewa kafin ta kai karshe. "Bana son sakarci kinji ko, wace irin magana ce wannan fita ki bani wuri" Rumana ta juya ta fita baki na radadi suka hada ido da Baaba Hure wadda ta gama jin hirarta da mahaifiyarta. A guje ta bar wurin tana tsoron ko kakarta taji abubuwan da ta fada. Sai dare Harisu ya dawo Baaba Hure ta zaunar dashi ta fada masa abin da Rumana ta gayawa Mamanta. "Tun da Rumana ta iya bushe ido da zuciyarta ina kara tabbatar maka da cewa da wuya idan karya take yi musu. Kafin abubuwa su kara lalacewa gara ka shirya kaje Abujan kamar yadda ka fadawa Maamun a waya kuyi magana da ita. Idan akwai cutarwa ta dawo nan muyi zamanmu. Ana uwar miji na gasa suruka ita kuma matar dan ce mara kirki " Harisu da baya son rigima yace "haba Baaba ai baki tabbatar ba. Ba don al'amura sun taso min ba ai da tun shekaranjiya zan tafi Abujan ma" Haka suka yi ta shawarar yadda tafiyarsa zata kasance jibi sannan ya tashi ya tafi nasa dakin. Rumana duk abin duniya ya isheta saboda kewar Maamu da halin da ta barota. ***** Kwance Gimbi take tana karkada kafa daya tana tunanin yadda take cin karenta babu babbaka. Yanzu jin kanta take yi daidai da kowa. Miji yana da kudi kuma yana tafin hannunta. "Uwarsa kuma ta zama hoto abin kallo." ta fada a fili tana murmushi. Kafin ta hanata zaman gidan mijinta ita tayi saurin maganin abin. Anti Bebi ce ta fado mata ta kwashe da dariya har da kyakyatawa. Ko ina take yanzu oho. Cikin dan lokacin da bai wuce wata guda ba ta gina fadarta yadda take so. Agogon wayarta ta kalla biyar da rabi ta dan wuce ta fito zuwa dakin Maamu. Tana zaune akan abin sallah ta kara ramewa duk ta dashe ta jingina bayanta da bango tana kallon fanka tana tunani. Jin muryar Gimbi a kanta ba karamin tsoro ya bata ba ta dawo da kallonta gareta. Sai da ta zauna a kusa da Maamu sannan ta kwalawa Rita kira akan ta kawo abincinta na rana. Ragowar dankalin hausa ne da aka soya musu da yara da Awaisu suka ci da farfaesu da safe tasa aka kawowa Maamun. Sai dai ita nata banda bushewar da ya fara babu farfesun sai yaji aka dan barbada a gefe. Idanunta da basa rabuwa da hawaye taji sun soma cikowa ta sunkuyar da kanta. Gimbi tayi murmushin keta ta janyo mata plate din tare da daukar daya ta dangwalo yajin. "Bude na baki a baki kinji Maamuna. Ai cewa Rita nayi yau kada a baki shinkafar rana saboda kada dankanoma ko basir su kamaki" Da yake hausar tayi mata tsauri da yawa bata fahimta ba ta bude bakin a dole saboda yadda take tsoron Gimbi. Dandanon yajin mai azababben fada ne ya fara sauka a harshenta kafin taji an tura mata dankalin dukkansa. Kwarewa tayi ta soma tari sai ga Awaisu ya taho amma daga bakin kofa ya tsaya yana tsoron kada ya karaso Gimbi tayi fada. Zuciyarsa babu dadi don yasan ba'a kyautawa Maamu amma cikin lokaci kankani sai yaji ya manta ko abin ya dena damunsa a rai. Kasa jurewa yayi yadda Maamu take cin dankalin tana kwarewa ko ruwa babu a kusa. Juyawa yayi zai tafi Gimbi ta kira shi tana wani shu'umin murmushi "Abban Haris yau ka ganmu a baki nake bawa Maamu abinci ko. Kasan nice 'yar gatanta kai ka nemi wata" Maamu ya kalla ya ga ta tsira masa idanu tana yi masa kallon ka ceceni. Ji yayi kafafunsa har rawa suna yi ya fice batare da ya tankawa Gimbi ba. Yana tafiya Maamu tasa kuka Gimbi tayi ta rarrashinta wai me take so. Da ta gaji ta fito falo suka kebe da Rita. "Madam wai yaushe zaki mayar da matar nan garinsu tunda aiki yayi kyau ita da Oga duka a hannunki suke" Dariya tayi "na fasa mayar da ita saboda wadannan munafukan dangin nasu masu sa ido. Gara mu zauna a nan tare irin haka bata isa tasa ko ta hana ba bare tayi min iko da gidan miji." Rita ta gyada kai "haka ne kuma" Bayan Gimbi ta shige wurin mijinta Rita ta tafi kitchen ta dauko robar ruwa ta kaiwa Maamu a daki. Tsayawa tayi a kanta tace ta sha ta bata robar kada Gimbi ta gani. Maamu sai da tasha rabin robar ta mika mata. Rita ta dan share kwalla. Daga ita har Ovi ba mutumci garesu ba amma ta fuskanci Gimbi lamba daya ce a rashin imani. Sosai take jin tausayin Maamu yana shigarta albarkacin yawan adduar da Maamu take yi na neman sauki. ***** Washegari da wuri Harisu ya sanar da Awaisu zai taho da safe ya nuna masa farincikinsa sosai kuwa. Wurin azahar sai ga waya daga Katsina garinsu Baaba Hure yayanta da take bi ya rasu. Cikin gaggawa suka shirya kusan rabin gidan suka kama hanyar Katsinan. A hanya Harisu ya sake kiran Awaisu yana fada masa. Yaji mutuwar domin yasan mutumin dattijon kirki ne. "In sha Allah ranar uku zai kama asabar zan taho Katsinan. Ka yiwa Baaba gaisuwa kafin na kira" Yana ajiye wayar Gimbi dake zaune a cikin office dinsa ta hade rai "ina zaka je?" Ta tambaya a gadarance. "Yayan Baaba ne ya rasu zanje Katsina" Ta kyabe fuska zata yi masa kuka "kai da ayyuka suka yi maka yawa nake so weekend dinnan ka samu hutu shine zaka tsiri tafiya. Haba Abban Haris ka tayani kula da mijina mana. Kana bukatar hutu. Next weekend sai muje Katsinan tare" "To" yace yana kallonta tana wani kwarkwasa kamar a gidanta. Ganin yana samun kudi sosai ga kasuwancinsa ko shi kadai suke dashi zasu wataya son ransu yasa ta ajiye aikinta. Amma kullum sai taje office din Awaisu kai masa abincin rana. Har an ganeta ana tsokanarsu da cewa soyayyarsu tana burge mutane. Ita kuwa mata ne bata so yayi mu'amala dasu don yadda ya kara kyau da haske saboda zaman naira kishinsa a ranta ya karu. Su Harisu sun isa Katsina nan suka zauna har akayi sadakar uku babu Awaisu babu wayarsa. Idan ya kira shi ma baya dauka sai can dare yayi masa text wai aiki yayi yawa. Jikin Harisu yayi sanyi so yake kawai ya ganshi a Abuja. Abokansa har na Fika sun zo gaisuwa ga Alh Saminu na Kano dashi suke komai sai kaninsa ne zaice aiki yayi masa yawa. Duk hakuri irin nasa baiji dadi ba ko kadan. Sun koma Fika da iyalansa ya bar Baaba cikin 'yan uwa tace sai tayi wata guda zata koma. Kwanansa biyu da komawa tunanin canjin da yake gani daga wurin Awaisu ya dame shi. Hada kayansa yayi ya kira babba cikin yaransa maza mai sunan babansu suna kiran shi Abba yayi masa rakiya zuwa Abuja. Suna isa kamar ya kira Awaisu ya fada masa sun shigo sai kawai ya fasa suka wuce gidan. Maigadi ya gane shi babu shamaki ya barshi ya shiga. Gimbi ta tafi park shakatawa da yaranta sai Rita a falo tana kallo. Sallama Abba yayi ta fito kofar wajen da dan skirt wanda da kyar ya rufe rabin cinyarta. Harisu ya sunkuyar da kai Abba yasa kai zai shiga ta hana wai bata sansu ba. Harisu yace mata shi yayan maigidan ne daga garinsu. Sai ta danyi murmushi "Kaine baban Rumana ko, duka sun fita mutan gidan amma Maamu tana ciki muje na kaiku dakin" Abba na gaba Harisu na bayansa suna bin Rita har kofar dakin Maamu. Dakin duk yayi kura saboda shigowar sanyi da gani ba'a sharewa. Wani sauti mai kama da kuka Abba ya saki wanda ya kai hankalin Harisu kan Maamu da Abban yake kallo tana tsaye a bakin gado. Wata tsohuwa ya gani tukuf don har tafi Baaba Hure nuna tsufa mai kama da Maamu. Sanye take da riga da zani amma saboda rama hannu daya ya sabule har kusan kirjinta. Fuskar nan ta koma tamkar kashi lullube da fata. Gabadaya ta rame sosai sai idanu sun firfito ga kasusuwan wuya. Zani ne a hannunta take kokarin daurawa yana ta sabulewa saboda rashin isasshen wurin da zai zauna. Kuka Harisu yasa tamkar karamin yaro yaje ya rike hannuwanta duka biyun ya durkusa yana bata hakuri. "Maamu bansan zantukan Rumana gaskiya bane...., har raina naso ace karya take yi dan uwana bazai wulakanta aljannarsa ba. Ki yafe mana Maamu, ki yafe mana " [15/08, 17:45] ‪+234 803 272 5896‬: *KASHE FITILA*💡 29 *Batul Mamman*💖 Kuka Maamu ta fashe dashi irin mai ratsa zuciyar nan. Duk wani bakinciki da bacin rai da take dannewa a lokacin ya bayyana. Kukan nata ya sake tayarwa da Harisu hankali. Abba yana tsaye daga gefe idanunsa shima sun kada sunyi jawur. Tsanar Kawun nasa Awaisu ce ta dirar masa a zuciya yana mai kara tabbatar da labaran da Rumana ta basu da ta koma. Bayan tayi shiru Harisu ya soma kokarin taimaka mata ta zauna a bakin gado fafur taki. "Maamu ki zauna muyi magana don Allah" ya fada muryarsa tana rawa. Yau da wani ya bashi labarin an ganta a wannan yanayin bazai taba yarda ba. Rama ce tayi tamkar ta shekara a kwance. Cikin muryar da ta dashe da kuka ta dafa kafadarsa "Harisu ka mayar dani cikin 'yan uwana kafin ku fitar da gawata" Agogon hannunsa ya kalla ya ga biyar ta kusa. Ya dan tausasa murya "In sha Allah gobe war haka kina dakinki a Fika." Hannu ya ga ta daga masa "Wallahi Harisu bazan kara kwana a gidan nan. Indai ina da sauran gata a duniya ko yaya ne kuma ina da kima a naka idon kayi min wannan alfarmar don Allah" Ji yayi ta kara karyar masa da zuciya ya kira Abba da ke tsaye kamar dogari yace ya bude drawer ya hada mata kaya. Kai ta girgiza ta dauko hijab dinta akan abin sallah. "Ni da nake jiran lokacina yayi me zanyi da kaya Harisu?" Maganar ta tsaya masa a rai sosai ta kara masa tausayinta. Wannan duniya ina zaki damu yake ta fada a ransa. Shi dai Abba ya rarumo duk kayan da hannunsa ya kai garesu. Haka suka fito suka nufi indai ya ajiye motarsa da ya tuko su. Itama Awaisu ne ya cika masa ya saya. Duk da cewa yayi matukar gajiya saboda baya dogon tuki haka ya sake shiga mazaunin dreba zai tuka su. Abba ne ya shiga rokonsa akan ya bari ya tuka yayi masa alkawarin bazaiyi gudu ba. Da kyar ya shawo kansa ya bashi mukullin bayan dogon gargadi. Da shigarsu gidan da sake kama hanyar Fika ko cikakkiyar awa daya ba'a samu ba. Rita tana ganin sun fita daga gidan ta sauke ajiyar zuciya. Burinta su fita kafin uwar gayya Gimbiya ta dawo. Wannan tsohuwa ba karamar wahala take sha a gidan ba. ***** Hayaniyar su Mu'allim ce ta sanar da Rita dawowarsu ta fito daga dakinta sanye da wani gajeren wando da riga damammiya mai karamin hannu. Gimbi ta saki baki tana kallonta kafin ta hau ta da fada "Wani sabon iskanci ne zaki fito min a haka lokacin da mijina ya kusa dawowa? Common go and change." Rita da bi jikinta da kallo sannan ta kalli Gimbi a yatsine sannan ta koma daki. Ita fa ba don Ovi ta nace tazo gidan ba babu abin da zaisa ta zauna ana mata cin kashi. Amma bari dai hakarsu ta cimma ruwa. A falon suka bararraje ana ta ciye ciyen kayan kwalama da Gimbi ta saya musu. Binsu take yi da kallo dadi na ratsa zuciyarta saboda yadda take son yaranta. Daula wadda ta tafi fitsari tun shigowarsu ta kwala mata kira daga ciki. Yanayin kiran yasa ta tashi da sauri ta nufi dakin da take. A korido suka hadu Daula tana nuna dakin Maamu "Mummy Maamu bata nan" Tsaki ta ja da karfi tana hararar yarinyar "saboda haka kike yi min wannan mugun kiran? Daga zuwa fitsari me ya kaiki dakinta" Daula ta sunkuyar da kai. Gimbi tayi gaba zuwa dakin Maamu tana ta surutai. Rashin ganinta a dakin bai dameta ba tayi tunanin bandaki ta shiga. Sai ta kula babu haske. Kamar ta fita sai ta koma ta buga kofar da karfi "Maamu" ta kwala mata kira kamar sa'arta. Shiru taji ranta kuwa ya baci. Jiya ta sake zuba mata wani maganin kwantar da zuciya wanda zata mallaketa kamar yadda ta mallake danta. Shine kuma taki amsa kiranta? Lallai da sake. Tura kofar tayi inda taji tsamin abinci ya bugi hancinta. Da sauri ta kunna fitila sai ga kwandon shara ya soma cika da abinci ya lalace. Baki Gimbi ta rike tana gyada kai "wato kwana ukun nan matar nan asara tasa na dafka. Kaddai ace bata cin abincin tun na ranar da na soma saka maganin" "Mummy me kika ce?" Daula ta kura mata idanu. "Babu komai kirawo min Rita" Bata jima ba suka dawo tare harda su Haris ta tsegumta musu Maamu bata nan. "Kinga fitar Maamu ne?" Murmushi da soma yi domin duk yadda Gimbi taso boyewa kana kallonta kasan hankalinta a tashe yake. Boka yace kada ta bari Maamu ta fita daga gidan. A haka ne zata fi iya juya Awaisu hankali kwance. "Anzo an tafi da ita" "Me?" "Waye yazo?" "Ina aka kaita?" A gigice take maganar Haris da yafi sauran wayo shima hankalinsa ya tashi. Amir kuwa kuka ya saka "Mummy ko saceta akayi? Sai da nace miki mu tafi da ita Park din kika ki" "Rufe min baki" ta daka masa tsawa sannan ta koma ga Rita ta sake tambayarta waye ya dauki Maamu. "Baban Rumana ne fa." "Harisu yazo gidan nan? Yaushe?" Yau ko dan jarida ya shafawa Gimbi lafiya a tambayoyi. Rita ta fada mata cewa sun zo babu kowa suka fito da ita suka tafi. "Haba Rita bayan kinsan komai yaya zaki bari su tafi." Wayarta ta dauka ta tafi daki harda rufe kofa. Awaisu ta kira tana kuka ta fada nasa Harisu yazo ya dauki Maamu batare da saninsu ba. Yana cikin office har lokacin ya nuna mata babu matsala zai kira shi dama sunyi magana. A harzuke tace "da saninka dama yazo. Shine zai tafi da ita don a nuna ni ban iya kula da ita ko me?" Jin ta fara fada ya soma bata hakuri. Haka nan ya hada kayansa ya tafi gida batare da yasan me zuciyarsa take ji game da tafiyar Maamu ba. ***** Duka 'yan uwan Harisu mata ya kira a waya yace komai dare idan mazansu sun amince yana bukatar su zo gidansa. Kowacce hankali a tashe ta nemi izini ta tafi. Sannan ya kira wani cikin yaran kawunsa da ya rasu yace a bawa Baaba Hure waya. Bayani yake son yi mata sai kuka ya kwace masa. Me zai fada to. Ya ga Maamu a yanayin da zaka rantse ta fito daga kasashen da yunwa tayiwa kamun kazar kuku ne. Rama ce irin wadda ake nuna mutanen a TV ace a taimaka musu rashin kwanciyar hankali a kasarsu ya hade da yunwa. Baaba ta razana sosai da jin kukansa. Mutum babba kamarsa yana kuka tasan babu lafiya. "Harisu kaine kake kuka kamar ba namiji ba? Me ya faru?" "Maamu ce" Zumbur ta tashi daga zaune ta tsaya baki na karkarwa "wani abun ne ya faru?" "Na daukota Baaba. Don Allah ki taho gobe" Baaba duk ta tsorata ko rasuwa tayi ya boye mata ta soma kuka itama. Maamun ya kalla tana kwance a bayan mota inda yayi mata pillow da babbar rigarsa. Idanun nan duk sun.shige loko sai jirwayen hawayenta yake gani yana jika rigar tasa. Wayar ya dan kara mata a kunne tayiwa Baaba Hure sallama. Ajiyar zuciya Baaban tayi tace mata gobe da asuba zata taso. Matarsa ta uku wadda dama yau girkinta ne ya kira ya sanar da ita suna hanya ta fadawa kowa. Sannan ya umarceta tayi abinci mai rai da lafiya yana tare da Maamu. Jin sunan Maamu ta fita da sauri ta sanar da abokan zamanta. Rumana na jin haka tace a bata mukulli zata gyara mata daki. Su Anti Baraka kusan tare suka shigo gidan da kannenta suna mamakin wannan kira na Harisu. kamar hadin baki ma da niyar kwana duka su ukun suka taho don sun san babu lafiya. Shadayan dare ta wuce suka iso kusan duka gidan aka fito tarbarsu. Motar yarabsuka kusan rufewa suna ihun Maamu tazo. Sai dai me. A bayan mota take kwance kai kace karamar yarinya ce saboda yadda ta kankance. Anti Ummukulsum ce tace kowa ya matsa ta mika hannu ta riko Maamu. Ai tana fitowa da ta kare mata kallo bata san lokacin da kuka mai sauti ya kwace mata ba. Nan fa sauran suka matso kowa ya ganta sai kuka. Maamu sai murmushin yake take yi "Ban mutu ba Kaltume, meye na kukan" Rumana kusan bangaje iyayenta tayi tazo ta rungume Maamu. Sai a lokacin Maamun ta soma nata sabon kukan. Harisu kasa hanasu yayi shima zuciyarsa tayi rauni. Da taimakon Rumana Maamu ta soma tafiya zasu shiga cikin gida sai ga zaninta yana neman faduwa saboda yayi mata yawa da nauyi ta kasa daurawa. Duk wanda ya kula da hakan sai da kukansa ya karu don tausayi. Suna shiga ciki dakinta aka kaita sannan aka kori yaran don sun cika dakin. Cewa tayi duk su dawo babu mai fita yau Allah Ya yaye mata kadaici. Abinci aka jere mata tuwon semovita ya tuku da kyau an kulla a leda da miyar kuka wadda taji daddawa da wake da naman kazar da tsabar dahuwa yasa ya soma fashewa. A wani flask ga kunu mai zafi sannan ga kayan tea da ruwan zafi da bread. "Idan akwai abin da kike so Maamu ki fada na dafa miki" cewar Anti wadda tayi girkin. Godiya tayi mata tace wannan ma ya isa. Wai ita ce da wannan kwanuka a gabanta duk nata ne taci iya cinta. Lallai ashe da ranka da lafiya da kuma matsayi da mukami lomar abinci ma sai Allah Ya yarda zaka samu. Ita da arzikin danta ya isa ace tana daukar dawainiyar wani ma ta fanin ciyarwa ita ce ta koma haka saboda yunwa. Rumana ce ta zuba mata abincin har lokacin tana zubar da hawaye da takaicin me yasa ta gudu ta bar Maamu. Dama sun dade da ramewa su biyun tun kafin ta taho amma abin yayi muni yanzu da ta ga Maamu. Abinci Maamu taci sosai ta kora da kunu sannan ta bukaci ruwan wanka don ko sallar magariba basuyi ba bare isha. Cikin 'yan matan kannen Rumana wata ta kai mata ruwa ta sirka mata. Mama ta kaita bandaki ta dawo suka hau maganar wannan abin al'ajabi. Harisu yana jinsu yace suyi shiru sai Baaba ta dawo gobe zaa san me ya kamata ayi amma tabbas zaman Maamu ya kare a Abuja. Suna wannan tattaunawar ne Rumana ta shigo a guje. Dama a kofar bandakin ta tsaya tana jiranta. "Baba ga Maamu can tana ta amai" A gurguje suka fito dukkansu suka nufi bandakin inda suka sameta a bakin kofar tana durkushe tana amai ta baki ta hanci. Cikin kankanin lokaci ta galabaita sosai tana neman fita daga hayyacinta. Abinka da mata sunfi yawa a ciki sai koke-koke da salati suke yi. Harisu ya kinkimeta Abba ya fito da mota ya sakata a ciki suka fice sai asibiti. ***** "So nakeyi ka kira Harisu kace ya dawo min da Maamu yadda yazo ya dauketa" Gimbi ke wannan furuci tana karkada kafa daga zaune a gaban Awaisu. A ladabce ya ke bata amsa "Kiyi hakuri nasan zai dawo da ita" ""Wai kai baka ji haushi bane yazo har gidanka don gadara ya dauke maka uwa. To meye nufinsa?" "Naji haushi mana, tunda ranki ya baci nima naji haushi amma nasan baiyi da wata manufa ba. Don ma ina ta kiransa ne bata shiga da tun dazu na ce gobe ya dawo da ita" Tsaki ta buga masa ta tashi. Gashi dai ta mallake shi amma ita bata jindadin yadda ya zama baya iya wani tunanin kirki akan komai sai tayi magana. Maimakon yaji haushi sai wani shirme yake yi mata. [15/08, 17:45] ‪+234 803 272 5896‬: *KASHE FTILA*💡30 *Batul Mamman*💖 Wani asibiti suka nufa nan cikin garin Fika. Suna zuwa Harisu ya dauko Maamu ya shiga da ita. Likita aka kira yana ganin yadda take ya fara bawa nurses umarni. Haka suka rinka guje-guje a dauko wannan a dauko wancan. Ba su suka samu ta dan daidaita ba sai gabanin asuba don sumanta biyar. Likitan kansa ya jigata. Harisu ya nema yace lallai su kaita babban asibiti a cikin Damaturu don gaskiya tana cikin mawuyacin hali. A ambulance aka sakata suka bi bayansu shi da Abba da Anti Baraka. A hanya suka kira gida wanda suma duka sukayi kwanan tashin hankali suka fada musu an canza asibiti. Dama ana kokarin hada musu abin karin kumallo ne. Suna isa gado aka turo domin daukarta ganin a ambulance aka kawo mara lafiyar sun san abin babba ne. Wata likita ce akan Maamu tana ta gwaje gwaje. Jininta ma da kyar aka samu don an bulata yafi sau shida basa samun jinin yadda suke bukata. Maamu ta galabaita iyaka don ko magana ta kasa yi sai hawaye akai akai da yake zirarowa ta gefen idanunta. Kusan awa biyu sannan likitan ta fito ta tafi office dinta tana yarfe gumi. Tun kafin ta fita iyalin Harisu suka iso suna ta koke-koke don kallo daya zaka yiwa Maamu kayi tunanin kafin ka matsa ta cika. Cikin yaran ma mutum uku aka taho dasu harda Rumana wadda tafi kowa kuka. Idanunta sun kumbura sosai ga ciwon kai matsananci. Wani mutum wanda da alama masinja ne yazo ya kira Harisu zuwa ofishin likitar. Yana shiga godiya ya fara yi mata amma bata ko amsa ba ta jefo masa tambaya. "Mene ne tsakaninka da mara lafiyar nan?" Dan gyara zama yayi yana tsoro me zata ce ya sami Maamu "Babata ce" "Babarka? Babarka?? Amma shine...." Ta soma magana murya na rawa sai ga hawaye shar. Hannuwanta biyu da ta dora akan tebur din gabanta tasa ta rufe fuskarta. Harisu yayi mamaki sosai don sai da ta kwashi kusan minti uku kafin ta ita daidaita kanta ta dago jajayen idanu tana masa wani irin kallo cikin bacin rai "Lokuta da dama sai ace likitoci suna kashe marasa lafiya bayan kune ba kwa tashi kawo su asibiti sai lalura ta cinyesu" Harisu ya dubeta "hakane likita amma kowa kika gani baya rasa dalilin faruwar hakan" Dr. Yana bata san lokacin da ta daga murya ba don ba karamin haushin 'yan uwan Maamu taji ba a irin yanayin da ta ganta. "Malam babarka tana cikin mawuyacin hali zaka ce kana da dalili? Wannan ciwon fa ba na lokaci daya bane" hannu tasa ta fara masa lissafi da yatsunta "Kaga da farko jininta yayi mugun hawa ina tsoron Allah Yasa kada ta sami matsala a zuciya, na biyu ulcer tayi mata mugun kamu har kirjinta ta taba, na uku malaria ta jima da shigarta baa dauki mataki ba. Na karshe shine malnutrition. Wallahi kun zalinci matar nan ba kadan ba" Duk da fada take yi wani hawayen ne ya taso mata. A awa biyun da ta tsaya kan Maamu tasan ba karamin jin jiki take yi ba. Matar da ko tari ta kasa yi saboda kirji ya rike. Dr. Yana mace ce mai matukar tausayi da jinkai. Asibitin suna ji da ita. Duk tausayinta kuma a tsaye take bata bata sake da aikinta. Idan kaji ana Dr. Barrister to da ita ake don idan taga mara lafiya kamar akwai cutarwa cikin lamarinsa to fa ta tsaya masa kenan ayi ta dauki ba dadi da ita. Zuwanta kotu yafi a kirga bada shaida idan aka cuci mara lafiya. Shi dai Harisu tunda ta hau lissafi yake salati. Karamin tsaki ta ja don a ganinta aikin banza ne. Da can baa kula da ita ba sai yanzu da ciwo ya gama cin karfinta. Mikewa tayi tsaye tana masa nuni da kofa "muje ka sallami masu kukan nan domin damunta kawai zasuyi. Sannan akwai irin abincin da nake so a rinka bata musamman madara saboda ulcer din." Kai ya gyada ya bi bayanta. Haushin Awaisu yake ji ta yadda da zai ganshi a lokacin baiga wanda ya isa ya hanashi kai masa duka ba. Anya yana ma cikin hankalinsa kuwa. Maamu ce fa mahaifiyarsa. Matar da aljannarsa take tattare da farincikinta. Da suka karasa kofar dakin sanar dasu yayi su tafi dama shima kukan nasu ya ishe shi. Nan suka fara shawarar masu zama tunda akwai tafiya. Suwaiba autarsu Harisu da uwargidansa aka bari. Yaso zama suka dage akan lallai ya tafi gida ko wanka yayi saboda tafiyarsu ta jiya. Rabonsu da abinci shi da Abba tun jiyan kafin su kama hanyar Abuja. Sai da sukayi musu siyayyar kayan bukata musamman na Maamu suka dau hanya da alkawarin dawowa da sassafe. ***** Tsaki Gimbi tayi don ganin Awaisu har yanzu yana kwance tun bayan sallar asuba akan abin sallah. Tsaya masa tayi a kansa ta soma mita "Hala dai yau baka da niyar zuwa aiki?" Kansa ya rike duk da a kwance yake "Gimbi I feel sick. Jikina duka babu kwari ga fargaba da take damuna na rasa dalili" Jin ya dauko zancen da take so yasa ta zauna a gefensa ido ya ciko da kwalla zata yi masa kuka "Nasan rashin Maamu a kusa da kai ne yake damunka. Ni kaina abin ya dameni. Kuma ko ka yarda ko kaki yarda dan uwanka bai kyauta ba. Maamunmu ko shine ta haifa tunda a gidan nan take bai kamata ya dauketa bamu sani ba." Shiru Awaisu yayi yana nazarin maganarta. Ta kuma rissina kai ganin zancen ya soma shigarsa. "Ni yanzu ta yaya gidan nan zaiyi min dadi babu Maamu? Na riga na saba da ita kamar mahaifiyata. Tana bani shawarwari wanda naga amfaninsu sosai. Ko ba don kanka ba ka dawo min da Maamu zanfi samun kwanciyar hankali " Kukan munafurci ta rinka yi hawaye kamar famfo. Hankalin Awaisu ya tashi yayi ta bata hakuri da alqawarin zai dawo mata da ita. A gabanta ya rinka kiran Harisu yaji shiru ba amsa. Yace tayi hakuri zai kara nemansa zuwa anjima. Murmushi tayi masa ta fita daga dakin. Zuciyarsa ya ji ta sake shiga kunci sai dai ya rasa meyasa tafiyar Maamu tayi masa dadi maimakon yaji bacin rai. Har kasan zuciyarsa yana jin zamanta wurin Harisu ya fiye masa kwanciyar hankali. ***** Bayan kwana biyar Rita tana goge falo taji sallama. Bata ankara ba Haris ya taho a guje har yana bangajeta saboda muryar da ya gane. Wadda ya gani ya nufa da gudu sai kuma ya tsaya turus alamun kunya an fara zama samari ya kasa karasawa. Murmushi ta sakar masa kafin tayi magana su Daula taji suna kokarin kayar da ita. Rungumesu tayi don tayi kewarsu duk irin tsiyar gidan. Ihun yaran ya fito da Gimbi daga daki da waya a kunne suna magana da wata kawa da tayi a gidan Bokan Ovi. Sakin wayar tayi ba shiri tare da wangale baki a dan tsorace "Laminde" Laminde ta dan murmusa fuskarta babu yabo babu fallasa. Jikin Gimbi yayi sanyi ta daure tace yaran su saketa haka ta wuce ciki su gaisa sosai. Laminde ta bi bayansu suka shiga ciki. Ajiyar zuciya tayi da ta tuna yininta na karshe a gidan da yadda al'amura suka kasance. Rabonta da Abuja tun da aka sallamota daga asibiti gashi har an bawa shekara baya. Da ta koma gida ne Allah Ya kawo mata miji tayi aure. Karamin ma'aikaci ne a wani kamfani amma an basu gidaje a Quarters din kamfanin kanana saboda nisa. Shine tazo ganin su Maamu. A kan kafet ta zauna Gimbi tana ta tsaneta da idanu har sai da tayi danasanin zuwa. Har ga Allah lamarin Maamu ya tsaya mata a rai kuma shine musabbabin zuwanta ta duba baiwar Allah. Gimbi ta hakimce akan kujera sannan ta sa yaranta suka bar falon suna ta kunkuni. Bayan sun fita ta kalli Laminde "Ince ko dai lafiya kika zo. Idan aiki kika dawo ni na dade da daukar wata" Laminde ta kalli Rita. Mace har mace tasa kananun kaya irin wannan tana yawo a cikin gida wai 'yar aiki a zamanin nan da kafin shaidan yazo zukata sun riga sun gama rauni da sabon Allah. "Na shigo garin ne na leko mu gaisa" tana magana tana dan waige waige ko zata ga giftawar Rumana ta tambayeta Maamu. Tabe baki Gimbi tayi "basa gidan wadanda kika zo ganin. Sai ince a gaida gida ko tunda ba wurinmu akazo ba" Laminde ta fahimci korarta akeyi ta soma haramar tafiya. Wani dan saurayi taga Rita ta shigo dashi yana ta dariya suka gaisa da Gimbi da gani sun saba wasa da dariya. Tape ya dauko dama da bironsa a saman kunne yace "Hajiya Gimbi sauri nakeyi fa kizo na gwadaki na bar mutum yana jirana a waje" Sam ta ma manta da Laminde bata fita ba tace "Kezy ka rainani fa. Ni zan karaso nan ko kai zaka zo" Da murmushinsa ya karasa gabanta ta mike tsaye. Karamin mayafin da yake kanta ta daure a saman kan dama bai kare komai ba. Nan tela ya hau gwajin dinki fa. Haka ta rinka daga hannuwa yana zagayeta tana cewa so take rigar tayi mata das a jiki saboda dinkin kece raini za'ayi. Laminde ji tayi wani abu ya tsaya mata a wuya. A cikin ranta ta zabgawa Anti Bebi tsinuwa. Tabbas ko da can Gimbi ba wani kirki gareta ba amma ko kadan halayyarta bata yi kama da ta Gimbin yanzu ba. Sa kai tayi zata fita ta kusa karo da mutum. Da sauri ta kauce Awaisu ya shigo baya ko ganin gabansa da kyau don ko bi ta kanta baiyi ba bare yaji gaisuwar da take yi masa. Gimbi ya kalla da Tela ana nan ana ta gwaji amma ko a jikinsa bare ya hana. Laminde da tayi zaton za'ayi tashin hankali akan wannan gwajin wulakancin sai taji yace "Inata kiran wayarki baki amsa ba" Ta dan bata rai "tana daki bana son damu ne" "Ai gara ki rinka hutawa. Dama takarda aka kawo office dinmu zan cike sunayen masu zuwa workshop Lagos jibi. Shine nayi ta kira in tambayeki nasa sunana ko kuwa" Kezy Tela ya kwalo idanu yana jin ikon Allah. Duk tsagerancinsa abin ya daure masa kai. Gimbi ta kula dashi da Laminde mai tafa hannuwa daga kofar shigowa falon sai ta fakaice da cewa "amma dai abban Haris ka iya rigima. Wato don kada nace ka tafi ka barni ko. To na yarda kasa sunan amma idan kaje babu ruwanka da yan mata" Kai ya dan rissina yana mata godiya ya kuma fice. Laminde tabi bayansa ta tsaya suka gaisa da maigadi. Nan yake fada mata ko sati Maamu batayi da tafiya ba. Duk tausayin Maamu ya kamata tace ko akwai number da zata iya samunsu yace bashi da ita. Daga nan tayi masa sallama ta tafi. ***** Dr. Yana ce ta kalli su Baaba Hure tana ta bata rai "wai don Girman Allah waye wannan Awaisun ne? Haba baiwar Allah tun da ta farfado kullum sai ta kira shi kunki ku kawo mata shi. Mara lafiya na bukatar kulawa bare ma ita da abu yake neman kaiwa zuciya. Indai ba mutuwa yayi ba ku kira mata shi don Allah" Maamu tana daga kan gadon sai kalmar mutuwa taji ai kuwa ta soma kuka tana cewa shikenan ta kashe shi. Anti Ummukulsum ta gallawa Dr. Yana harara. "Wai ke wace irin likita ce kullum sai anyi fada dake a dakin nan. Dame kike so taji ne. Ciwon ko irin wannan maganganun naki" Nurses biyu da suke tare da ita suka soma dariya. Indai da sabo su kam sun saba da jajibo rigima irin na Dr. Barrister. Kanta tsaye take gabatar da komai nata shiyasa wasu basa fahimtar ta. Ga yan uwanta kuwa cewa akeyi gaboncin 'ya'yan fari ke damunta. Tsuke baki tayi ta maida hankalinta ga Baaba Hure. "Iya don Allah idan da hali ku kira mata wannan Awaisun ku huta itama hankalinta ya kwanta mu samu ta warke da wuri. Kwanaki haka aka kwantar da wata a dakin nan kuma kan gadon nan ma itama tayi ta kiran mijinta iyayenta suka ki sanar dashi wai saboda ya sakota. Ranar nazo dubata tace in fada masa ya yafe mata amma sharri kishiyar ta kulla mata. In gaya miki washegari ta cika. Iyayenta suna ta kuka da mijin yazo yana son neman gafararta ya gano gaskiya suna cewa da ma sun sani sun hadasu sunyi maganar karshe gashi ta tafi ba'a cika mata burinta ba" Harisu yana bakin kofa zai shigo yaji tana wannan labarin ya rike baki. Kullum burinta ta tsorata su ne, me zai sa ta rinka dauko zantuka irin haka. Shi kam dole ya nemi babba a asibitin a canja musu likita. Baaba Hure tana hada ido dashi ta taso "Harisu don Allah ka sanar da Awaisu halin da Maamu take ciki kada ta cika bai nemi gafararta ba" Dr. Barrister ta murmusa daga gefe. Ko da bata jin yaren taji an ambaci Awaisu ga kuma alamun tsoro a idanun Baaba Hure. Ba don Maamu na jin jiki ba so take ta tambayeta labarinta taji kwaf don a yanzu duka bata yarda dasu ba. A ranta tace kowa cikinsu mulmul dashi sai ita kadai a wannan mawuyacin yanayin. Bayan ta fita ne Harisu ya zauna a gefen gadon Maamu yana kare mata kallo. Tun zuwansu jininta yaki sauka shi kuma yayi rantsuwa bazai kira Awaisu ba kamar yadda ko waya idan yayi masa baya dauka. Duka 'yan uwansa ya umarcesu kada su kuskura su sake daukar wayarsa. Idan ya damu da ita ya biyo bayanta. Baaba Hure tace ita dai idan har ta isa dashi to a yau take so ya kira Awaisu ya fada masa. Zuwansa ko rashin zuwan ya rage nasa. 'Yan uwan Maamu suma Harisu yace da farko kada a fada musu sai ta dan murmure don a haka bai san inda magana zata tsaya ba. To a yadda Dr. Barrister ta tsorata Baaba suma sai tace a fada musu. Tunda yanzu idan ta rasu basu da madogara zaace ya daukota babu wanda ya sani. Dan kallonta yayi sannan yayi murmushi tare da kwafa "waccan shu'umar likitar duk ta birkita miki lissafi. Zanyi yadda kika ce Baaba in sha Allah" Sauran 'yan uwansa dake dakin da iyali suka goyi bayan a sanar din shi yafi ko don gudun zargi nan gaba. Duk abin da akeyi Rumana tana gefe don kullum sai tazo saboda shakuwarsu da Maamu. Shima Harisun baiyi tunanin hanata ba. Tausayin Maamu take ji sosai a ranta ta fita daga dakin ta bar iyayenta suna magana. Wani dakali ta zauna tana ta tunanin irin ukubar da suka sha a Abuja. Dr. Yana ta dawo daga wurin Director na asibitin yayi mata kashedi sosai akan yiwa marasa lafiya katsalandan ta fito rai a bace tana kumburi. Rumana ta hango kuma ta gane yarinyar mai shegen kukan nan ce a dakin da ta baro dazu. Wani birki taja tare da komawa ta dafa kafadar Rumana. A dan firgice ta dago sai ta maida kai da ta gane wace. Dr. Yana ta zauna a gefenta ta fara mata nasiha akan cuta ba mutuwa bace da sauransu. Sai da ta gama ta hau bugun cikin Rumana akan alakarsu da Maamu. Rumana an sosa mata wurin da yake mata kaikayi nan fa ta hau bayani tana kuka ta zayyanewa Dr. Barrister alakarsu da zaman birnin tarayya da suka yi. "Jakar uba....amma kuna da hakuri wallahi. Har naji babanki yayi daraja a idona " Saurin dagowa Rumana tayi wanda yasa Dr. Barrister ta dan wayance "kara daraja yayi nake son cewa. Dama da darajarsa na ganshi" Tashi tayi ta koma office dinta tana ta tunani. Gaskiya taimakon irin wadannan jihadi ne fa wanda bata so a barta a baya. Kai dole ma ta shiga a dama da ita saboda wannan dattijuwa mai siffar salihan mata bata cancanci cin kashi daga wurin surika ba. "Yadda kika kashe fitilar zuciyarta ina mai tabbatar miki da taimakona kece zaki zauna a cikin duhun ba ita ba" ta fada a fili tana kallon ceiling din office dinta. [15/08, 17:45] ‪+234 803 272 5896‬: *KASHE FITILA*💡32 *Batul Mamman*💖 Bayan kamanin rabin awa aka bude kofar dakin. Tura Maamu suka ga anayi akan gado tana kwance ko kwakkwaran motsi bata yi. Kuka ne ya barke daga bakin matan da ke wurin domin duka matan Harisu da su Aunty Suwaiba sun iso. Baaba Hure ce tayi karfin halin hanasu a lokacin Harisu ya bi bayan likitocin. Dr. Yana tasan yana binsu shiyasa bayan sun daidaita Maamu a I.C.U ta fito ta same shi. Yanayin barkwancin nan duka babu afuskarta sai tausayi. Ita ta soma magana da ta karaso inda yake tsaye hankalinsa a tashe "Mun samu jikin nata ya dan daidaita. Ta kusa samun heart attack ne dazu" "Innalillahi wa inna ilaihi rajiun. Dr yanzu menene abin yi?" "Addu'a ita ce za'a cigaba da yi. Sannan gaskiya ku dena taruwa da yawa a dakin tana bukatar hutu. Wannan dakin bama bukatar kowa sai mutum daya itama kuma ba ciki zata zauna ba." Godiya yayi mata ya juya ya tafi da niyyar hada kansu su tafi gida ta kuma tsayar dashi "Awaisun nan da take kira har a cikin wannan tsananin ciwon addua take yi masa. Don Allah a karo na karshe kada kace na shiga abin da babu ruwana ku taimaka ku kawo shi. cuta ba mutuwa bace amma tana jin jiki." Jiki a sabule ya koma kofar dakin nan suka tsare shi da tambayoyi. Ya gama yi musu bayanin me likita tace yayyen Maamu maza suka zo da matansu har da su Tikeke da Bomai kanin baban Awaisu. Harisu yaso sakaya lalurar Maamu amma Baaba Hure tayi musu bayani dalla-dalla. Nan wurin ya kaure da salati sai da security yazo yace duk su koma waje. A nan ma manyan suka hado aka yanke shawarar su wuce Fika ayi maganar a gida. Mazansu da matansu manyan haka suka hadu a falon Harisu ana fadar abubuwan da suka faru. Baaba tasa aka kirawo Rumana domin shaida. Ita kuwa bata boye komai ba dangane da yadda suka tsinci kansu a gidan Awaisu. Bomai da ake ganin yafi kowa shiririta ne ya soma magana bayan an sallami Rumana. "Lallai biri yayi kama da mutum. Idan kun tuna zuwanmu gidan nan abubuwa marasa dadi sun faru. Kuma daga bayanin wannan yarinya Rammana duk mai hankali yasan cewa akwai wata a kasa" Wanda Maamu take bi ya amshe "abin da ya faru ya riga ya faru sai dai mu kiyaye gaba. Dama Maamu ga zurfin ciki tazo ta hadu da bacin rai dole ya taba zuciya. Ni dai idan da mai zuwa ya kamataa gobe muje mu taho da Awaisu ko yana so ko baya so" Kowa yayi na'am da wannan shawarar inda aka yanke cewa zasu tafi su uku harda Harisu da Bomai. Can asibitin kuwa Aunty Baraka ce ta zauna ko da zaa bukaci wani makusancin Maamu. ***** Da yake jirgin safe Awaisu ya biyu kafin azahar ya iso gida. Yana zuwa ya tarar Gimbi bata nan ga yara sun tafi makaranta. Rita ce ta fito da gudu tana yi masa maraba kamar zata rungume shi. Abin ya bashi tsoro ma yayi saurin matsawa baya sai tayi murmushi ta wayance da karbar jaka. "Sir how was your trip?" Fine yace kawai yayi gaba. Saurin shan gabansa tayi ta matso daf dashi tana karairaya "ga abincin na gama hada maka" A gajiye yake baya son yin magana shiyasa ya wuceta kawai yana mamakin wannan abu da take yi kamar zata shige jikinsa. Ita kuwa dariya tayi tana tunanin lokacin da nasu aikin zai fara aiki ta shigo gidan ayi waje da Gimbi. Dakinta ta koma ba jimawa taji ana buga kofa da karfi. Ita da Awaisu kusan karo suka yi suna sauri zuwa bakin kofar don jin ko lafiya. Bashi hanya Rita tayi yana budewa suka hada ido da wata mace da jikinta duk ya motse ga fuskarta kamar ayi amai saboda lalacewar fata. Tana tsaye tana ta susa tana bige bige a jikinta. Maigadi yana bayanta yana son tabata ya fitar da ita amma kyankyami ya hana. Ganin Awaisu yasa ta dan sakin rai "Awaisu fadawa wannan yaron gidan naka cewa nice Anti Bebi" Sake kallonta yayi cikin rashin gaskata me take fada. Wannan matar da ko almajira bata kai matsayin a kirata dashi ba itace Anti Bebi. Yana cikin wannan tunanin yaga ta rike wuya tana ta kakari. Da kyar ta saki wuyan tana haki "Shegu yanzu kuma wuyana akace ku shake. Duk abinku ni Bebi nace dubu sai ceto" Maigadi ne ya kuma yunkurin miko hannu sai suka ji horn a waje. Da sauri ya tafi ya fita duba waye ya bar Awaisu da Anti Bebi da Rita. Anti Bebi ta dan nutsu ta soma magana "Awaisu ta inda aka hau ta nan ake sauka. Ka fadawa Gimbiya naji labarin komai daga wurin aljanun da tasa suke bibiyata kuma wallahi dani take zancen domib bata ci riba ba. Yadda tasa nake dandanar balai a rayuwata itama ta shirye gamuwa da nata. Nayi alkawarin ko zanyi yawo tsirara ne sai naga bayan Gimbiya" Su Harisu ne suka shigo ta karamin gate din mai tafiyar kafa. Karshen maganar Anti Bebi kawai suka ji suka kalli juna. "Nasan bata nan shiyasa na shigo amma idan na kuma shigowa sai nayi ajalinta" yawu ta tofa a kasa ta juya ta fita suna mata kallon mahaukaciya. Sai a lokacin hankalin Awaisu ya kai kan bakin nasa. Da faraarsa ya taho yana musu sannu da zuwa. Bomai ya kalli Rita da kayan jikinta "Yanzu Awaisu meye wannan a gabanka?" Harisu yace "mai aiki ki" Yayan Maamu ya daure fuska ya kalleta yace ta basu wuri. Awaisu ya nuna musu kofa su shiga ciki suka ce a'a. Kawun nasa yace "ba zama muka zo yi ba Awaisu. Ana ta kokarin sanar da kai Maamu bata da lafiya kaki zuwa." Harisu ya kalla yayi wani murmushin takaici "yanzu abin harda su Kawu kuka hada a ciki? Me na rage ku dashi da har zaka kalawa Maamu cuta kawai don kuna son na zo Fika na baku kudi? Idan kana bukatar wani abu kafi kowa sanin cewa a shirye nake na baka" Ba su Kawu ba hatta Harisu bai fahimci zancen ba sai da suka nemi yayi musu karin bayani. Nan ya fada musu abin da Gimbi tace Amir ya fada ya kara da cewa yasan bazata taba yi masa karya ba. "Kazo ka dauke Maamu ka bar min mata cikin damuwa kawai saboda son abin duniya..." Wani wawan mari irin wanda Awaisu baya jin an taba yi masa tunda yazo duniya Harisu ya kwada masa a kumatun hagu yana huci saboda tsantar bacin rai. "Ni Awaisu? Ni kake fadawa magana irin wannan?" Bacin ransa da haushin Harisu wanda ya rasa dalilinsu ne suka kara tsanani a zuciyarsa har hawaye suka fara fita daga idanunsa ba tare da ya sani ba. "Saboda na fadi gaskiya shine zaka mareni? da me na rageka da zaka sanya mahaifiyata cikin son zuciyarku kai da Baaba Hure" Ran Harisu ya kara baci yayo kan Awaisu a harzuke. Kwalarsa ya kama da hannu daya da daya hannun kuma ya rinka marinsa shima kuma hawayen yake yi. Muryarsa tana rawa yake magana ga su Bomai na son ya saki Awaisun ya ki. "Awaisu nine Harisu...ka dawo cikin hayyacinka ka kalleni. Yayanka ne wanda zaiyi komai domin farincikinka da rike amanar da Mahaifinmu ya dauka." Tamkar karamin yaro Awaisu yake zubar da hawaye ya ma dena kokarin kwacewa daga rikon da Harisu yayi masa. Kirjinsa ya dafe yana kallon dan uwan "Yaya kirjina ne yake min zafi kamar ana hura wuta. Na rasa abin da yake damuna. Yaya ka taimaka min" Harisu rungume shi yayi tsam a jikinsa yana shafa masa baya shima kuma yana hawayen. "Allah baya bacci Awaisu. Ka roke shi zai kawo maka sassauci cikin lamuranka" Bomai da Kawu suka ja gefe suna kallon wadannan 'yan uwa. A hankali cikin sigar lumana Harisu ya sake labartawa Awaisu ciwon Maamu sannan ya roke shi ya zo su tafi ya dubata. A ransa yana son zuwa amma zuciyarsa tana ta hura masa wutar kada ya yarda da yayansa. Ba karamin yaki yayi ba da tsananta karanta Hasbunallahu wa ni'imal wakeel da Lahaula wala quwwata illa billah sai ya sami kansa da amincewa. Su Kawu suna murna Harisu yace yaje ya dauko kayansa su tafi yace zuciyarsa bata so ya shiga gidan. "Yaya kullum da tsoron gidan nake kwana. Amma bari naje na dauko mukullin motar da wayoyina da wallet " Su ukun suna waje kusan minti shabiyar sai gashi ya fito har da yar jakar kaya. Rita ta biyo bayansa tana tambayar ina zaije ya daka mata tsawa akan ta dena binsa. Wata jeep ya nufa ya kira maigadi ya dan gogeta suka shiga suka fice. Rita duk ta kidime tayi ta kiran Gimbi shiru bata daukar wayar. Yau tasan gidan babu zaman lafiya. ***** Daga saloon Gimbi ta fito taje anyi mata kananun kitso da karin gashi da dan mayafinta a rabin kai irin na Anti Bebi babu dankwali ta fito zata shiga mota. Daga tsallaken titin tun daga nesa Mama ta hangota suna dawowa daga unguwa da Umar. Da sauri ta rinka dukan kafadarsa tana nuna masa Gimbi akan suje wurin da sauri kada ta tafi. Wata irin kwana yayi har suka kusa gwara motocin ta kuwa fito a fusace tana bambami. Mamaki ne ya isheta ganin Mama da kaninta ta dan murmusa. Ba karamin kewar mahaifiyarta tayi ba. Sai dai taji kunya sosai don rabonta da gida tun ranar da ta koma gidan Awaisu da kanta. Sannan ko waya bata taba yi musu ba. "Idonki kenan Gimbi?" Ta dan rausayar da kai "Mama nayi zaton kuna fushi dani ne shiyasa na kasa zuwa gidan. Yaya kuke da Alhaji?" Kaninta ta kallo da ko fitowa daga motar baiyi ba bare tasa ran zai kulata ta murmusa ta leka ta window tayi masa magana kawai sai ya saka waya a kunne shina dole baiji ba. Abin ya bata mata rai sosai kuwa. Kwanakin nan ba karamin kewar 'yan uwanta take yi ba da iyaye. Mama tace "ban sani ba ko kin hadu da Bebi amma tazo min a kamanni na ban tsoro tana ikirarin ganin bayanki. Gimbi shawara ta karshe zan baki domin indai da rai baa fitar da rabon samun gafarar Allah. Ki tuba ki dawo daga rakiyar wannan mummunar rayuwa da kike yi. Ni da 'yan uwanki babu mai zuwa gidanki wannan umarnin babanki ne. Amma ki sani yadda Bebi tauraronta ya haska har ki mutu bana jin zaki kamota. Yau ga Bebi duniya ta gwada mata ita budurwar wawa ce. Wanda duk ya kamu da sonta a sannu zata yaudare shi ta karar da duk wani abin arziki a tare dashi sannan ta gudu ta barshi." Shiru Gimbi tayi tana tunanin su Mama basu san wanda ta kama ba. Bokanta na yanzu ba dai ta fadi bukata ba kafin kace kwabo zaka ga yadda kake so indai an kiyaye sharuddansa. Bata samu bakin magana ba Mama ta shige mota suka tafi suka barta a tsaye. Motarta ta shiga ranta a dagule ta kula da wayarta tana haske. Ko da ta duba missed calls din Rita sunfi biyar. Kiranta tayi don tasan babu lafiya. Ai kuwa ta bata mummunan labarin tafiyar Awaisu. Wani zagi ta rinka jerawa Harisu sannan ta tada mota tayi gida. Kafin ta karasa Ovi tazo don a hanya tayi mata waya. Tambayarta shawara tayi akan me ya kamata tayi Ovi tace da safe ta hada kan yaranta su tafi Fika don kada tayi bakin jini "Ki sani ko an fadawa boka babu yadda zaayi ace an rufe bakin kowa a cikinsu. Tafiyarki kawai itace mafita. Idan kinje ki san yadda zakiyi ki kwantar da kai a wurinsu sannan ko da Maamu ta fada musu wasu abubuwa ki karyata. Zani wurin boka gobe sai na fada masa a haukata ta idan yaso dole a yarda dake. Mijinki kuma kada ki damu shima zaa sake daure miki shi" Ovi na fita Rita tabi bayanta "Sis yaya zaki bata shawara haka mu sai yaushe zamu fara namu aikin?" Ovi ta dafa Rita ta rage murya "kada ki damu wannan shawarar babu inda zata kaita. Kuma bazani wurin Boka ba don gobe ma ni Enugu zamu tafi da wani sabon kamu da nayi " Tafawa sukayi sannan Ovi ta fice. ***** Awaisu ke tuki babu mai magana cikinsu har suka isa wani gidan mai suka tsaya yin sallah. Daga nan Harisu ya karbi tukin Awaisu ya zauna a gaba kusa dashi sai bacci. Yana baccin nan banda mugayen mafarkar babu abin da yake yi. A firgice ya farka ya cigaba da kallon titi. Damaturu suka wuce suka nufi hanyar asibitin. Gaban Awaisu ne ya rinka faduwa akai akai tun kafin su karasa har Harisu yayi parking. Ji yake kamar bashi da laka ga mugun tsoro ya mamaye zuciyarsa. Hannunsa yaji Harisu ya kama suka nufi ICU. [15/08, 17:45] ‪+234 803 272 5896‬: *KASHE FITILA*💡33 *Batul Mamman*💖 Har suka isa kofar dakin Awaisu a tsorace yake. Dayake kofar ta glass ce ta wajen Harisu ya nuna masa Maamu kwance tamkar bata da rai. Wai a haka ma ta danji sauki kuma ta dan murmure ba kamar lokacin da aka kawota ba. A hankali ya taka ya leka inda Harisu ya nuna masa. Kafafunsa ne suka fara rawa sai gashi yana neman faduwa. Harisu yayi saurin tare shi sai dai yana mikewa ya fice daga cikin asibitin zuciyarsa tana matsanancin harbawa. Jikin motarsa yaje ya shiga ya rufe kofar sannan ya kifa kansa akan sitiyari. Kuka Awaisu yake yi sosai irin wanda rabonsa dashi tun kuruciya. Kukan da yake yi ba na halin da ya tarar da Maamu bane , kuka ne na tsananin nadama da tausayin kansa. Idan ya mutu a yanzu ya tabbatar bashi da abin da zai kare kansa a gaban Mahallicinsa. Tambaya daya yake ta nanatawa a zuciyarsa. Shin yana ina Maamu ta kamu da ciwokan da Harisu ya fada masa ya daukota dasu? Wata faduwar 6gaba ya sake ji da ya tuna rabonsa da sata a ido tun wata waya da ya hadata da Harisun farkon komawar Rumana Fika. Mahaifiyarsa abokiyar sirrinsa, abokiyar shawararsa ita ce a wannan yanayin kuma a cikin gidansa bai sani ba. Innalillahi wa inna ilaihi rajiun yayi ta maimaitawa a ransa. Shi dai ba jahili bane. Ya san cewa wurare da dama a Al'Qurani Allah SWT Yayi umarni da bin iyaye da kyautata musu. Hadisai kuwa bazai iya kirga wadanda ya sani masu magana akan bin iyaye ba musamman uwa wadda ta sha wahalar ciki, haihuwa, raino da kula da 'ya'yanta tun zuwansu duniya har sai ta dena numfashi. Uwa ko kana ganin kaiune maiyi mata komai na bukatun rayuwa baka taba girmaa idonta shiyasa ko a gidanka take bata fasa yi maka tambayoyi kamar kaci abinci ko kana jin bacci. Tunaninsa na karshe shine yanzu idan Maamu ta rasu a wannan yanayin yasan duniyarsa ta gama lalace, lahirarsa kuma dama ba'a magana. Share idanunsa yayi ya koma cikin asibitin. Dr. Yana tana tsaye da su Harisu ana kokonto ko Awaisu tafiya yayi sai gashi ya dawo. Ganin likita a wurin ya roketa ta taimaka ta barshi ko na minti biyu ne ya shiga wurin Maamu. Harisu ta kalla da guntun murmushi a fuskarta "Shine Awaisu?" Shi ya amsa mata da kansa "nine don Allah ki bari na ganta" Bude masa kofar tayi ta matsa gefe tana murmushi. Maamu tana kwance tana tunanin yadda rayuwarsu ta sauya cikin dan lokaci. Ga kudi sosai Allah Ya basu amma Ya jarrabesu da mace irin Gimbi wadda ta kasa gane me ta tsare mata. Kamar a mafarki ta jiyo kamshin turaren Awaisu wanda ta dade da saninsa dashi. Tana ayyanawa a ranta wane likitan ne mai wannan turaren taji an kama hannunta an rike gam. A hankali ta bude idanunta suka sauka cikim na Awaisu. Cikin wata irin murya mai rauni yace "Maamu" sai ya kawai ya durkushe a gefen gadon yana kuka. Ita ma Maamun hawaye take fitarwa a hankali ta dora hannunta daya a kansa tana shafawa. Sun dauki kusan minti biyar a haka wadanda suke wajen dakin harda Dr. Yana suna kallonsu wasu suna tayasu kukan. Sake dago kansa yayi bakinsa har rawa yake yi. Maamu ta rame iyakar rama. Idanuwanta duk sun shige ciki ga uban baki da tayi. "Ki yafe min Maamu. Don Allah kada fushinki ya zama katanga gareni da samun rahamar Allah." Murmushi tayi cike da jindadin addu'arta ta karba hankalin danta ya dawo jikinsa tasa hannu ta goge masa wasu sababbin hawayen da yake fitarwa a hankali "Ban yi fushi da kai ba domin nasan baka san abin da kake yi ba" Girgiza kai yayi "so nake kice kin yafe min Maamu. Nayi miki alkawari wallahi bazan kara saba miki ba. Daga yanzu har karshen rayuwata akan rokon gafararki da kyautata miki zanyi" Lumshe idanu tayi a hankali "na yafe maka Awaisu. Allah Ya cigaba da tsareka daga sharrin mutum da aljan. Allah Ya yafe mana baki daya" Yana kuka yana dariya ya rinka cewa ameen. Ji yayi wani sakayau jikinsa kamar an zare masa wata kaya mai sukarsa a zuciya. Daga shi har ita babu wanda ya sake magana sai lokaci zuwa lokaci su kalli juna suyi murmushi. Shi Awaisu ma har jin ya rinka yi kamar ya zama sabon mutum. Kusan awarsa daya a dakin kafin Dr. Yana ta sake dawowa tace ya fito a bar Maamu ta huta. Ba don yaso ba ya fita yana jaddada mata cewa a kofar dakin zai zauna tare da su Baaba. Haka ya fito yana tunanin dole ya koma Abuja ya fara processing kai Maamu asibiti a Egypt ko Saudiyya ko kuma duk inda aka tabbatar masa akwai manyan likitici da kyakkyawar kulawa. Gaban Baaba Hure ya fara zuwa ya durkusa ya gaisheta. Itama neman ta yafe masa yayi tana kuka tace ta yafe. Daga nan ya gaishe da su Anti Baraka da sauran 'yan uwa da suke zazzaune a wurin. Kallonsa suka rinka yi cike da tausayawa. 'Yan Harisu da na 'yan uwansa mata da suke wurin suma duka suka gaisheshi banda Rumana. Ya kula suna hada ido wata muguwar harara ta jefa masa tare da dauke kai. Dan murmusawa yayi ya matsa kusa da inda take zaune akan katon kafet din da suka shimfida a wajen. "Umm Ruman babu magana?" Ga mamakin kowa tsaki taja mai sauti kuwa ta tashi ta bar wurin. Bata yi nisa ba kukan da take boye ya fashe har suna jiyota. Mamanta ce ta kirata cikin fada tace wace irin dabi'a ce wannan. Mama uwargidan Harisu ta janyota jikinta tana goge mata ido itama hararar Awaisun take yi ta kada baki tace "ai dai baza'a daki mutum a hanashi kuka ba ehee. Kiyi hakuri kinji Rumana" Awaisu ji yayi jikinsa ya kara sanyi ya matsa gefe wurin yayansa yana kara fada masa abin da ake ciki dangane da ciwon Maamu. Ranar sai wurin shadayan dare suke kama hanyar Fika. Ba don an matsa masa ba nan yaso kwana a kofar dakin Maamu. Ita kuwa wannan ganin kawai da tayi masa ya sanyaya mata rai hankalinta ya kwanta. ***** Har shabiyun dare babu wayar Awaisu balle text. Gimbi ta kalli wayarta a karo na ba iyaka tayi jifa da ita tana fada ita kadai. "Wallahi Awaisu baka isa ka wulakanta ni ba. Don ka tafi garinku shine bazaka kirani ba?" Har wurin biyun dare ta kasa bacci tunani ya isheta. Bata kula da lokaci ba ta kira Ovi a tsohon daren nan. Cikin magagin bacci ta dauka tana tambayar me ya faru. A hargitse Gimbi take tace "babu lafiya Ovi. Kince kada na kira Awaisu boka yace aiki zai lalace. To amma kinga shiru yaki kirana. Ina tsoron fa kada su juyar masa da kai game da ni komai ya lalace." Ovi tayi siririn tsaki don ta ma manta da karyar da tayiwa Gimbi dazu sannan ta daure ta bata amsa "Kamar yadda na fada miki gobe kawai ki bi bayansa . Gara kowa ma yasan cewa basu isa dashi ba naki ne ke kadai. Ki tafi ki taso shi a gaba ku dawo gida" Cikin zakuwa Gimbi tace to. A nasa bangaren ji yayi ko kadan baya so yana tunaninta don fargaba hakan yake saka masa. Sannan duk da bai fada mata ba yayi mamaki da har ta kai yanzu babu wayarta domin jin ina ya tafi. Wasu abubuwa game da zamansu da Maamu ya rinka tunawa abin yana daure masa kai. Zarginsa akan Gimbi ya kara karfi amma bazai dauki mataki ba sai ya tabbatar saboda wannan abu ba karami bane da za'a yanke hukunci da gaggawa. Da sassafe ko abinci bai tsaya ci ba yace asibiti zai tafi. Hakan yayiwa su Baaba dadi ya tafi shi kadai. Baaba tasa aka kira Antu Ummukulsum da ta kwana ranar akan cewa yana isowa ta tafi gida domin a bawa da da mahaifiya damar ganawa a nutse. Harisu da ta bawa sakon murmushi yayi yana jindadin hali irin na tasa mahaifiyar. Ba karamin jinjina mata yake ba domin ita ce tushen zaman lafiyar gidan. ***** Kafin tara na safe Gimbi ta gama hada kayanta da na yara duka. Makaramtarsu tayi niyar fara zuwa sanarwa zasuyi tafiya. Suna zaman jiran dreban ya iso Ovi ta kirata bayan sun sake shawara da Rita. "Munyi magana da Boka yace kada ki kuskura kije garin nan sai yayi kwana biyar da rabi bai dawo ba. To daga daidai wannan lokacin sai ki hau hanya ki bi bayansa saboda sharrin makiya daga can garin nasu" Gimbi ta danyi jim tana tunani. Gashi ance kada ta kira yanzu kuma kada taje. Anya bazata janyowa kanta matsala ba kuwa? Shirunta yasa Ovi gane me take tunani tayi saurin cewa "Kada ki damu yace aiki zaiyi akan mijin naki da babat tasa yadda zasu tsani juna. Zuwanki yanzu zai bata masa aikin ne" Sai a lokacin hankalinta ya kwanta tayiwa Ovi godiya sukayi sallama. Ovi ta kira Rita tace tayi maza taje ta fadawa bokan yadda sukayi da Gimbi koda zata zo kada ya karyatasu. ****** A rana ta biyar da tafiyar Awaisu Gimbi ta shirya tahowa Fika. A can kuma Maamu tana ta samun sauki don har an mayar da ita amenity. Yanzu har hira anayi da ita kuma ta soma cikowa. Awaisu shanu biyu ya saya yasa aka yanka kullum ana sarrafawa a kawo mata. Suma jamaar gidan sun sami nasu rabon. Kaji da kayan lambu da na marmari kuwa wani na tarar da wani. Barin kudi yake yi kamar bai san ciwonsu ba. Burinsa kawai Maamu ta warke ya cigaba da kyatata mata. Yau bayan ya dawo daga sallar azahar ya tarar da Dr.Yana a dakin. Wajen dakin ya biyota bayan ta gama duba Maamu da barkwancinta yace yana son fitar da ita waje yana bukatar takardun gwaje gwajensu domin tafiya dasu. Dan daure fuska tayi "a haka kuke sawa muji babu dadi. Yanzu duk kokarin da muke yi kuma ciwon bai gagaremu ba shine zaka ce zaka fitar da ita?" "Baki fahimceni bane, ina so ta sami kulaw ne sosai saboda wasu dalilai nawa" Dariya tayi ganin yadda yayi da fuska da gaske yake. "To don Allah ka bari ta kara samun sauki sannan ko fitar zakayi da ita sai kayi." Godiya yayi mata ya koma cikin dakin. Rumana wadda har yanzu bata kula shi tayi saurin mikewa zata fita. Girgiza kai yayi ganin da gaske yarinyar nan fushi take yi dashi "Rumana ina zuwa?" Kamar yayi magana da dutse ko girmansa bata gani ba tayi hanyar kofa. Ai kuwa manyan dake dakin suka hauta da fada ta fita a fisace tana hawaye. Tasan har abada bazata taba manta rayuwar gidan Awaisu ba. Idan ta kalli Maamu haushin kanta na barin gidan ita kadai take yi da kuma na Awaisu da ya gagara kula da ita. Maamu na kallonta ta kalli yadda ya bita da kallo wai itama ta zama 'yan mata ta iya fushi. Daga inda take zaune ana bata abinci tace ya bi bayanta ya rarrasheta. Anti Suwaiba tace ya rarrasheta ko ya zane ta dai "yarinya taki sakawa ranta salama kullum fushi" Maamu ta sake kallonsa "idan ka taba min ita zamu sa kafar wando daya da kai da yayar taka mai bada shawarar" Anti Suwaiba na dariya ya fita yana cewa yanzu duk duniya ai babu da mai ladabinsa. Ya dan wahala wurin nemanta kafin ya hangota can wurin ajiye motoci a durkushe tana share hawaye. Wurin ya karasa tana ganinsa ta kuma tashi sai dai kafin ta fita ya rufe hanyar. Dama tsakanin wasu motoci biyu ta zauna a wani dan tudu wanda bayansa fence ce babu hanyar fita. A tsiwace tace "zan wuce" Yana kada kai yace "Rumana..." Bai kare magana ba ta fashe da wani irin kuka mai tsuma zuciya. Idan da zata tona abubuwan da Maamu ta rinka dannewa a zuciyarta a zamansu a gidansa bata jin ko ruwa zai kara sha da dadin rai. Gabadaya komai ya sire mata har tsoro take ji kada itama ta girma duk yadda tasan Awaisu yana son Maamu ya koma haka itama ta zama hakan. Tausayi ta bashi sosai ya mika hannu zai rungumeta sai kuma ya fasa. Wannan ba 'yar karamar Rumanan nan bace. Shi bai san ma yana ina yarinya yar shekara goma sha shida ta zama 'yan mata haka ba. Da hannunsa ya nuna kansa ya dan rage murya "nine ko? Kiyi hakuri Umm Ruman Uncle Awaisunki bazai kara bari abin da ya wuce ya kuma faruwa ba" Baki ta dan tsuke "ni ba Uncle Awaisuna bane" "Har kin manta haka kike fada a gida kice naki ne ke kadai? Muje a tambayi su Baaba idan mun koma gida " "To na fasa ba nawa bane" Kwaikwayonta ya sami kansa da yi yace harda yin alamun kuka yace "don Allah kice naki ne ko na fadawa Maamu" Dariya yaso bata sai ta wani gimtse fuska wanda ya lura da hakan. Inda ta baro yace tazo su zauna ta fada masa duk abin da ke ranta ko zata sami sauki. Dr. Yana da take tsaye a jikin motar Mujahid tun dazu ta sauke ajiyar zuciya ta shiga. Kallonta yayi yace sannu da shanya ta dan kwanto a jikinsa tana fada masa wani kyakkyawan gamo tayi wanda dole ma ta ga faruwarsa. [15/08, 17:45] ‪+234 803 272 5896‬: *KASHE FITILA*💡31 *Batul Mamman*💖 A hankali take taku kamar ba ita bace mai aiki da kuzari a asibiti. Tana taka kafarta a kofar falo taji ana kokarin kinkimarta. Dariya ce ta subuce mata domin da kyar ya iya rabata da kasa kafin ya ajiyeta yana maida numfashi da kyar bayan ya sanya hannuwansa duka biyu ya rike gwiwoyinsa a duke. "Wai fa irin dan surprise dinnan zanyi miki na dagaki sama na juya ina miki wakar i love you. Gaskiya nauyi ne dake matar nan..." Tana dariya tace "kamar shari'a ko" Sai kuma ta dan bata rai "yanzu ni irin daukan da maza ke yiwa matansu sai dai na gani a tv" zama tayi harda tagumi ita a dole bata ji dadi ba. Kusa da ita ya zauna tare da sakala hannu a kafadarta "banda abinki wannan daukan da kike gani duk buge ne fa. Indai matar ba bugun fulawa bace katuwa a ido shafal a hannu to sai dai idan mijin kakkarfa ne jikan Antaru" Dariya sosai Yana da Mujahid suke yi ta mike "bari naje na gaishe da Hajiya sai na dawo ka fada min nice bugun fulawar ko kuma kaine rago baka cikin jikokin Antaru" Kamar yace ta dawo yadda suke nishadin nan haka yaji yana kallo ta fita ta zagaya bayan gidan bangaren mahaifiyarsa. Ajiyar zuciya yayi ya gyara kwanciya akan doguwar kujerar falon yana jiranta. Da sallama ta shiga wata mata da zata girmeta sosai tana durkushe gaban Hajiya tana kwaba lalle a wata roba ta amsa. Hajiya kuwa dauke kai tayi ta cigaba da sakace hakorinta. Yana ta durkusa ta gaisheta ta kara kawar da kanta gefe. Mai kwabin lallen wadda musamman yayar Mujahid ta daukota tana biyanta ta rinka taya Hajiya zama idan Yana ta tafi aiki tace Hajiya ana gaisheki . Da ido daya ta kalli Yana ta tabe baki "anje an gama gantali da sunan aikin an dawo? To sannu da zuwa sarauniyar masu gida" Murmushi tayi domin ta saba da halin surikar tata wadda ta kasance yaya ta uwa daya uba daya ga mahaifiyarta. "Hajiya yaya gida da sanyi sanyin nan?" Kin amsawa tayi sai ta janyo kafarta daga bangaren Laraba mai aikin nata ta dorawa Yana akan cinya saboda a kusa da ita ta durkusa. "Kinga cire mayafin nan zakiyi ki saka min lalle." Laraba tayi saurin janyo robar daga hannun Hajiya mai shirin turawa Yana "Haba Hajiya da ganinta yanzu ta dawo ki bari nayi miki ita taje ta dan huta" Wata uwar harara Hajiyan ta doka mata sannan ta fizge robar lallen "aikinta ne dama ba don ta sawa zuciya kwadayi ta gagara zama tayi bautar aure ba me zaisa ma a daukoki. Ga gida har gida ana neman shekara biyu taje tana bankar tarkacensu na asibiti nasara ya hore musu kunne anki haifa min jikoki." Yana kanta a kasa ta soma shafa mata lallen a kafa idanunta fal hawaye taji Hajiyan ta cigaba da fada "Ke nifa da ace ba Mujahid bane kadai namiji babu abin da zai kawoni gidansa. Yo gidane banda yahudanci da nasaranci babu abin da ake yi. Ni dai hadin zumunci baiyi min rana ba. Da bare ya aura mai halin nan da tuni tasan inda dare yayi mata. Yanzu kuwa ko me nayi sai ace babu kara babu zumunci. Ko ita uwar taki Yakaka ai tasan ina kokari" Cikin siririyar murya tace "Hajiya kiyi hakuri" Tsaki tayi tace ita dai a saka mata lalle kuma ta rinka yi daki daki kada wani wurin yafi wani kamawa. Mujahid da yake daga wajen dakin yana jinsu ya koma bangarensu zuciya babu dadi. Samun mace irin Yana sai an tona. Matar da bata da burin da ya wuce ta kyautatawa mutane. Idan ya nuna rashin jindadinsa game da yadda Hajiya take yi mata ranar kwana take yi tana fushi dashi. A cewarta bazata taba jindadin rayuwa ba idan ta zama silar da mijinta yayi wasa da aljannarsa dalilin kin kyautatawa mahaifiya. Zaman jiranta yayi sai bayan awa biyu ta dawo. Tana shigowa dundu tayi masa a baya tana fara'a kamar ba ita ba. Wanka suka yi sannan suka ci abincin da tayi musu kafin ta fita aiki. Suna gamawa aka kira magariba ya fita sallah ita kuma bayan ta idar ta gaggauta dora tuwo wanda ta gama kafin isha. Da ya dawo ne suna hira take bashi labarin Maamu da taji a wurin Rumana "Yaya ba don cin fuska ba nake baka labarin nan amma gaskiya wasu matan basu iya samun wuri ba. Yanzu ita Allah Ya bata wadda zasuyi zaman fahimta ga zuria amma ta daukowa kanta balai da hannunta" Hannuwanta ya rike tare da kokarin hada ido da ita "Kanwata don Allah kada naji kin shiga wannan case din. Nasan halinki na tarar aradu da ka. Amma har yau ban manta mutumin da kika taimaki matarsa akaje alkali ya kashe auren saboda dukan da yake mata. Kinfi sati ba kya fita daga gidan nan saboda fakonki da ya rinka yi. Ni kaina a tsorace na rinka fita kada a sabauta ni" ya kare da dariya Jinsa kawai take yi amma ko kadan bata tsammanin yadda labarin nan ya shigeta zata dauke kai. Ita fa salihancinta daya ne a rayuwa gaban uwar miji. Daga nan kuwa bata ki a hau sama a rikito ba indai zata kwatarwa mutun yanci. Yadda ya kula tana juya kai yasan maganar bata shigarta. Girgiza kai yayi don yasan aiki ya same shi. ***** A gaggauce Awaisu yake ta shiri ya watso kaya daga wardrobe yana cusawa a karamin akwati. Takun Gimbi yaji gabansa ya fadi sai dai ya dake ya cigaba da zubawa amma a hankali. Kallonsa tayi tare da akwatin "Indai kayan tafiyarka Lagos ne na hada maka tun jiya" In'ina ya soma sannan da kyar ya iya saita kansa yace "nasan wancan kayan duka suits kika zuba. Ni kuma yanzu Fika zan tafi na fasa zuwa Lagos din." Duk da ta razana ta daure tace "bangane ba" "Ashe tun daren jiya Yaya Harisu ke kirana Maamu tana kwance a asibiti. Bansan yadda akayi wayar ta koma silent ba sai da safe naga text dinsa" Gimbi ta hade girar sama da ta kasa. Dama ita tayi silencing wayar da ta ga Harisu yana kira "yanzu don sun rainaka shine tun tafiyarsu baa nemeka ba sai yau zasu ce Maamu babu lafiya. Anya ba wani abu suke kullawa ba? Kayi tafiyarka Lagos din kawai Abban Haris ina zaton maganar da Amir ya fada min bayan dawowarsu daga Fika kwanakin baya gaskiya ne" "Me ya fada miki?" Ya tambaya yana kokarin zuge karamin akwatin. Shiru Gimbi tayi taki magana. Awaisu ya sake tambayarta sai kawai ta fashe masa da kuka. Hankalinsa ba karamin tashi yayi ba domin kuka take mai cin rai. Duk yadda zatayi kada ya tafi sai tayi domin gudun bacin aikin boka. Zama yayi yana ta rarrashinta har zuwa lokacin da idea tazo mata sannan ta fara magana murya a dashe. "Kasan tun bayan dawowar Maamu garin nan ka rage zuwa Fika." Kansa ya gyada yana cigaba da kallonta. "Dasu Amir suka dawo shine yace min wai yaji Kawu Harisu da Baaba suna cewa yanzu ka rage basu kudi tunda Maamu tana nan. Wai zasu san yadda zasuyi ta koma Fika dole ka rinka zuwa" Jin haka ya mike da sauri rai a bace "bari naje na sami Amir din naji gaskiyar zancen nan" Kafin ya kai kofa Gimbi ta riko shi tana wasu hawayen "kada ka tambaye shi saboda ranar da ya fada min baka ga irin dukan da nayi masa ba nace bana son gulma. Nace masa kuma yayi min alkawarin bazai sake zancen ba" Hannunwanta ya zame daga jikinsa ya sake nufar kofa "ai ba wani zai fadawa ba sai ni." Har ta fara tsorata tace "amma Abban Haris baka ganin bata tarbiya ne hakan. Ni nace yayi alkawarin barin zancen kai kuma zaka sa ya fada. Kaga zai tashi da rashin sanin girman alkawari" Har zuciyarsa yasan ko kadan bai gamsu ba amma kuma zuciyarsa tana ingiza shi akan ya hakura. Wani irin bacin rai ya rinka ji ya juya a fusace ya dauko jakar da ta zuba masa kayan zuwa Lagos ya fita. Wani asirtaccen murmushi tayi a fuskarta kuwa tsantsar damuwa ce kawai take nunawa. Har waje ta biyo shi tana bashi hakuri akan kada ya dauki zafi da su Harisu 'yan uwansa ne. Shi dai bai tanka mata ba ya shige bayan mota dreba ya ja. Dakinsa ta koma ta daka tsalle tana murna. Su Harisu basu isa su dagula mata lissafi ba. Tasan duk ranar da hankalin Awaisu ya dawo jikinsa akwai rikici tsakanisu. To amma ko kadan bazata lamunce uwar miji ta rinka juya mata miji ta zama borar karfi da yaji ba. Aure tayi don taji dadi bata fatan irin zaman da wasu suke yi iyayen miji su mayar dasu tsumman goge goge. Mace ta kasa sakewa a gidanta saboda suruka me kenan akayi. Gara da tayiwa tufkar hanci taci karenta babu babbaka. Awaisu kuwa tunda suka fita zuciyarsa take masa wasu sake saken banza. Har ayyana masa takeyi Harisu ya killace Maamu ne kawai don yaci kudinsa. Abin haushin shine duk nemansa saboda su da iyalinsa ne. Me ya ragesu dashi da zasuyi masa haka? Numbar Maamu yayi niyyar kira sai wata zuciyar ta hana shi. Tsaki kawai yaja ya lumshe idanunsa har suka isa bankinsu. Aiki zai dan rage kafin lokacin tafiyarsu airport yayi. ***** Kwanaki biyu a tsakani Harisu ya cika fam da bacin rai. Ya sake kiran Awaisu wai shi yake fadawa ayyuka sunyi masa yawa yanzu ma yana Lagos. Harda cewa ya duba accout dinsa yayi masa transfer na dubu dari biyu su kara a kudin asibiti. Da wannan takaicin ya tafi asibiti yana zuwa Baaba take tambayarsa yaya sukayi da kaninsa ya daure fuska kuwa. Ganin haka Maamu ta soma hawaye. Bacin ranta ba na komai bane sai yadda danta ya juya mata baya. Harisu ya kula da haka ya dawo kusa da ita ya zauna yana murmushi. "Maamu ki dena saka damuwa a ranki. Kina warkewa da kaina zanje Abuja na sami Awaisu. Yanzu kinga likitoci sunce baa son komai ya bata miki rai. " Baaba ta kara da cewa kada ta damu tare zasu je sai wannan Gimbin ta gane bata da wayo. Ita dai jinsu kawai take yi tana yake don nuna musu bata damu ba. Suna haka Dr. Yana ta leko dakin da fara'arta suka gaisa ta tambayi jikin Maamu. Bayan ta dubata ta ne ta dan kalli Harisu wanda a cewarta bata ga mutum mai karamcinsa ba. "Uhmmm dama nace an kirawo mata Awaisun da take kira kuwa? " Baaba Hure tace "amma wannan yarinya da fitina kike. Yanzun nan mun samu hankalinta ya dan kwanta zaki zo ki tada zance." Langabe kai Dr. Yana tayi tana kallon Maamu "ni wallahi tausayi take bani. Idan yaki zuwa ne wani ya bishi mana a fada masa bata da lafiya yazo kada Allah Ya raba ganawar" Harisu ya dafe kai yana kallon yadda yanayin Maamu ya sauya tana neman kara rikicewa. Tsawa ya dakawa Dr. Yana yace ta biyo shi waje. A zuciyarta tayi dan murmushi bukatarta ta biya. Sumsum tabi bayansa suka koma can reception suka tsaya daga gefe. Hannuwansa biyu ya hada a gabanta yana roko "don Allah likita ki tsaya a iya duba jikinta ki dena tado mana zantukan da zasu hanata warkewa da wuri. Idan da kinsan irin wahalar da tasha za ki tausaya mata ne" Dr. Yana ta dago kanta ta gyara fuskarta alamun ba da wasa tazo ba. "Tunanin hakan ne yasa nake ganin ya kamata duk yadda zakuyi ku taimaketa kuyi. Bazan boye maka ba gaskiyar magana wannan baiwar Allah da wuya ta tashi. Ka dubi yadda jikinta gabadaya ya bushe ga cututtuka sun hadu da tsohon kashi. Idan kuka tsaya dogon tunani rai yayi halinsa baku hadata da Awaisun nan ba ku kanku bazaku ji dadi ba" So take ta sanar dashi tasan komai amma tana gudun yadda zai dauki abun. Tana kallo ya zurfafa a tunani tace "ko kasan ganinsa yana daga cikin abubuwan da zasuyi saurin kwantar mata da hankali ta sami sauki da wuri? Kuyi tunani akan shawarata. Indai yana da rai duk yadda zakuyi ku kawo mata shi ku kawo shi ko yaya ta saka shi a ido" Tana kaiwa nan tayi gaba. Rumana dake tsaye a bayansu dauke da kwanakan abinci ta goge kwallarta. Ita da kannenta ne Abba ya kawo su. Ji tayi ta sake tsanar Uncle Awaisu sosai. A iya sani da fahimtarta kawai yayi kudi ne yake wulakanta mahaifiyarsa da danginsa. Karasowa sukayi suka gaishe da Harisu sannan suka wuce. Maamu tana nan jiya iyau sai damuwa da ta karu. A cikin halin ciwo take sanar da Baaba Hure tana zargin akwai hannun Gimbi a wannan halayyar ta Awaisu. Abubuwa da dama da suka wakana a Abuja ta bata labari wanda itama Baaban ya kara tabbatar mata da zarginta na asiri ake yi masa. Hakuri ta kara bawa maamu da alkawarin Harisu zaije da zarar Awaisu ya dawo daga Lagos din da yace ya tafi. Da yake su kadai ne a dakin Maamu tana hawaye ta soma yiwa Baaba magana "Baaba kada kiga ina nuna damuwa kamar babu kara. Idan kika zauna a gidan nan yanzu ko yini daya ne zaki gane danki baya cikin hayyacinsa. Ina tsoron in mutu duk wani sauran zumunci namu ya yanke. Abubuwan da kuka yi mana bani da bakin saka muku ko godiya. Nayi tunanin Awaisu zai fitar dani kunya ya kyautata muku da zuciya daya. Sai gashi ni da na haife shi ma...." kuka ne ya kwace mata sosai sai tari ya sarke ta. Rumana tana daga waje duk ta gama jin abinda suke fada domin ta wuce sauran yan uwanta. Dama da kuka ta karaso na maganganun babanta da Dr. Barrister. Zantukan Maamu sun kara karya mata zuciya. Tana jin ta soma tari ta tura kofar ta shiga. Baaba ta gani rike da Maamu jikinta babu kwari tana ta tari. Dago kan da Maamu tayi daga cinyar Baaba sai jini suka gani yana fita ta bakinta. A razane suke duka su biyun Rumana ta soma kuka don tsoro ta kasa komai. Baaba Hure itama a tsoracen take tace "ki ruga ki kirawo min babanku da likita" Ta juya a guje zata fita taji muryar Maamu tana cewa "ki fadawa Awaisu na yafe masa" Bata jira jin karshen maganar ba ta fita. A hanya suka hadu da Harisu tana kuka ta fada masa Maamu na aman jini. Nan suka tafi shi da Abba kiran likita. Dr. Yana tare da wasu likitoci biyu suka taho dakin cikin sauri. Suna isowa suka sallamesu daga dakin suka rufo kofar. Jikin kowa a sanyaye suka tsaya jiran tsammani.[15/08, 17:45] ‪+234 803 272 5896‬: *KASHE FITILA*💡34 *Batul Mamman*💖 Cikin kuka Rumana ta rinka zayyanawa Awaisu wasu abubuwan da suka faru dasu a gidan. Ciki wasu ya sani har yana mamakin sai yanzu da take fada yake jin haushinsu. Me yasa a lokacin baiyi yunkurin daukar mataki ba. Ita ce tambayar da yayi ta maimaitawa kansa. Zuciyarsa ba karamin nauyi ta kara yi masa ba. Ba don a gaban Rumanan bane babu abin da zai hana shi kukan bakinciki. A raunane yace "Abin da yasa kika dawo gida kenan? Me yasa baki taba fada min ba?" Tambayar tasa ta biyu ce taji a kamar wani rainin wayo. Ita fa yanzu daga shi har matarsa tayi alkawarin dena ragawa kowa sai dai idan tayi a daketa ace mata mara kunya. Wani kallo ta bishi dashi kafin tace "Uncle a gabanka fa yawanci ake yi" Ajiyar zuciya yayi "haka ne....hmmmm...tashi ki koma ciki. Komai zai daidaita in sha Allah" Mikewa tayi tana tafiya yabi bayanta da kallo. Hakuri yaso bata na kasa rikonta da yayi sai kuma ya fasa kada sauran girmansa ya zube don ya tabbatar yanzu ba wata kima gareshi ba. Ita kuwa tana tafiya tana tuno wasu abubuwan da kunya tasa ta kasa sanar dashi. Yaushe zata manta cewa a iya zamanta na gidan kafin tayi rabin shekara ta koma yin gunzugu na mutan da da dankwalayenta saboda rashin kudin siyan pad. Daga baya ne da suka shaku sosai da Yusra ta fada mata shine take bata a makaranta. Tsigar jikinta ce ta tashi da ta tuna yadda take kasancewa duk wata. Awaisu bai bar wurin ba ya zurfafa a tunanin wannan rikirkitacciyar rayuwar tasa da ya kasa fahimtarta yaji wayarsa tana ringing. Kyalewa yayi sai da yaji mai kiran ya nace ya dauka. Muryar mace yaji tayi masa sallama a hankali ya amsa yana tunanin inda yasan wannan murya. "Shuhada ce, ka gane ni ko?" Ji yayi hankalinsa ya kuma tashi. Yaushe zai manta da ita, matar da Maamu ta dage sai ya aureta lokaci guda. Jin yayi shiru yasa ta kalli Daddynta da yake zaune kusa da Mamansu wadda ta dawo sati biyu da suka wuce. Alh Maitama ya mika hannu ya karbi wayar yayi masa sallama. "Suna na Alh Maitama mahaifin Shuhada" A mutumce Awaisu ya gaishe shi. A garin Abuja waye bai san wannan sunan ba. Tsoronsa daya ba dai maganar auren bace zasu sake tayarwa. Daga daya bangaren yaji Alhajin ya soma yi masa magana. "Malam Awaisu ina son haduwa da kai ne domin wasu maganganu masu mahimmanci " "Shikenan" ya fada a ransa yana tunanin tabbas zancen auren ne. A zahiri kuwa ya sanar dashi baya gari kuma bai saka ranar dawowa ba yanzu saboda rashin lafiyar mahaifiyarsa. Fatan samun lafiya yayi masa sannan yace "don Allah ka nemi ne idan ka dawo yanzu Shuhada zata turo maka nambar da zaka sameni. Ina kuma yi maka adduar yadda Allah Ya fitar dani kaima Ya fitar da kai lafiya. Sai naji daga gareka" Yafi minti biyu yana kallon wayarsa yana kokarin gano me Alh Maitama yake nufi da maganarsa ta karshe. Daga karshe ciki ya koma ya sami wuri ya zauna kusa da gadon Maamu. Idan ta dago kai sai ta ga yana yi mata kallo mai cike da tausayi. Murmushi kawai take yi tana ayyanawa a ranta ko yanzu ta bar duniya Alhamdulillah. ***** Bayan sun gama wayar Alh Maitama ya mikawa Shuhada wayarta. Mamanta Haj. Rahama ta ce "Daddy yanzu kana ganin zai yarda idan ka fada masa abubuwan da matarsa da Bebi suke yi?" "Ni da na yarda a yanzu nasan ba komai bane illa karfin addua da ikon Allah. Gabadaya jina nake kamar rayuwar da nayi da ita a mafarki ta faru. Lokaci yayi da matan nan zasu fuskanci hukuncin laifukansu. Dubi Shuhada duk irin son da mijinta yake mata Bebi ta shata musu layi bazasu kara zama tare ba idan har ba wani auren ta kuma ta fito ba. Kina ganin akwai iyayen da zasu so a rinka kirgawa 'ya'yansu aure ne?" Haj Rahama ta girgiza kai. Ita kanta Allah ne Yayi da sauran zama tsakaninta da masoyinta uban 'ya'yanta. Saki uku Anti Bebi tasa yayi mata daga shigowarta gidan. Fushin da tayi akan wannan sakin yasa tana gama idda tayi aure don ta nuna masa tana da sauran daraja. To da yake bata son mutumin zaman nasu yaki dadi ga kishiya can ma ta matsa mata. Auren bai jima ba ta fito. "Waccan ledar yaya za'ayi da ita ne" ta nuna ledar da aka kulle da tarkacen layoyi, guraye, ruwa kala kala a robobi da kananun tukwanen kasa duka dauke da sunayen Alh Maitama da iyalinsa. "Munyi magana da wani malami a islamiyar da su Shuhada sukayi. Yace zai zo karshen sati ayi addu'o'i sosai a gidan sannan a konasu." 'Yarsa ya kalla tana gefe tayi shiru sai ta kara bashi tausayi. "Ki kara hakuri kinji 'yar Daddy. In sha Allah da sannu Allah zai baki miji nagari. Jiya shima Tajuddeen nayi ta masa nasiha akan yayi hakuri ya fawwalawa Allah komai. Ni da kuka ganni duka abubuwan da suka faru kara min imani sukayi da sanin cewa lallai Allah Shi kadai Ya cancanci a bauta maSa." Sun jima suna hira wadda kusan dukkanta akan yanayin da suka tsinci kansu ne bayan zuwan Anti Bebi. Basu tashi ba sai da yayi musu alkawarin tafiya wurin Suhail cikin wata mai kamawa sai su jira ya kammala jarabawa su taho gida tare. Kudi kuwa ba kadan ya tura masa ba yace ya biya duk abubuwan da ake binsa na makaranta da bashin abokai idan yaci. ***** Yau Harisu ya tsaya a daya daga cikin shagunansa sunyi lissafi da yaron wurin. Yana dawowa Baaba Hure dama a shirye take ta fito su tafi asibiti cikin Damaturu. Sun kusa fita daga layin gidan nasu ta hango ta yi saurin cewa Awaisu ya tsaya. Juyowa yayi yana kallonta ta waiga baya "Wata na gani a motar can da ta wuce kamar Gimbiya" Ransa har ya baci jin sunanta yace "Gimbiya kuma Baaba me zai kawota yanzu?" "Juya mu koma gidan dai. Na tabbatar ita na gani" Ba musu suka koma. Ai kuwa suka hadu da Gimbi da yaranta a waje suna fitowa daga mota. Harisu da Baaba suka kalli juna ganin yadda ake ta fito da kaya daga boot. Kwalayen juice ne kala-kala da kayan abinci irin su shinkafa, maggi, taliya, mai da sauransu. Motar wata hadaddiya ce amma mai mazauni uku. Tana ganinsu Baaba ta dena yamutsa fuska musamman ganin yaranta sunyi wurinsu da gudu suna murna. Harisu yaji dadin ganinsu domin jinin Awaisu ne don yana kin babarsu baya jin akwai dalilin da zai sashi kin yaran. Gimbin ma da sauri ta karaso wurin Baaba ta fada jikinta tana ta murna. "Baaba mun sameku lafiya? Yaya gida ?" "Da kin bari mun shiga ciki sai gaisa sosai" Baaba tayi gaba yaran na biye da ita. Suna shiga ciki Gimbi ta nufi dakin Maamu tun a tsakar gidan take kwala mata kira kai kace 'ya tazo ganin babarta ne bayan sun jima basu hadu ba. A bude kofar take saboda an ajiye kayan wankinta da safe baa rufe ba. Ganin babu kowa kuma dama tasan babu din ta fito tana gaisawa da matan gidan. Su mamakin kayan da ake shigowa dasu sukeyi. Harisu ta kalla tana murmushi "Yaya Harisu shine daga zuwa ka dauke mana Maamunmu ko? To kafata kafarta tare zamu koma kuma mu hada da Baaba Hure kaga mun koma 'yan gata ko ta ina. Tana ina ne? Maamu???" Ta kare da daga murya tana kiranta. Murmushi Baaba Hure tayi wanda Gimbi tayi zaton na murnar tace zasu tafi da ita Abuja ne. A zuci tace kwadayayyu. Ita kuwa Baaba Hure tsabar mamakin rashin kunyar Gimbi take da gogewa a kissa. Tana kallonta tace "Su Makiru manya" Gimbi a razane ta kalli Baaba ba dai da ita take ba ta dan hade rai da tsoron kada a dagota. Baaba ta fahimce yadda fuskarta ta sauya ta daga kai tana kallon sama tana magana cikin kulawa da sassauta murya "Makiru shegen tsuntsu, idan baka iya takunka ba da ranka da lafiyarka sai ya sunkuce maka da ya barka da ciwon zuciya. Tsuntsaye da dama tsoronsa suke yi. Gimbi kuna dashi a Abuja? " Harisu ne yayi saurin magana saboda tsoron kada daga nan Baaba ta fadi maganar da zata janyo rikicia take a wurin don bata da hakuri indai an taba nata bisa rashin gaskiya. Yafi so cikin ruwan sanyi su shayar da Gimbi mamaki akan abin da tayi. "Babana ina Abbanku ne" ya dafa kan Mu'allim yana tambayarsa. Yayi sa'a babu kowa a wurin sai shi da Baaba kada wani yayi saurin cewa Awaisun yana nan. Gimbi tayi saurin cewa yaran "kai ku shige ciki" Bayan taga shigarsu dakin Maman Rumana ta dan tabe baki "Yaya Harisu lamarin kaninka sai addua kasan yadda ayyuka suke masa yawa. Tare muka so zuwa tun farkon tahowarku da Maamu sai aka tura shi Lagos. Na kasa hakurin jiransa ne nace bari na taho kawai kewar Maamu ta dameni. Shi kuma kwana biyar ban sami wayarsa ba ma, ina zaton aikin can din ne yayi masa yawa ko an sace wayar." Ikon Allah, wato da haka ta taho zata nuna bata san me yake faruwa ba kenan ta mayar da laifin kan mijinta. Girgiza kai yayi kawai yace "Allah Ya kyauta. Kuci abinci ku dan huta sai mu tafi Damaturu. Dama asibiti zamu je wurin Maamu muka ga shigowarku shine muka dawo" Jakar hannunta mai mugun tsada ta saki a kasa ta dafe kirji "asibiti kuma? Me ya sameta?" Bai kai ga bata amsa ba ta soma kuka harda daga murya. Nan da nan kuwa aka fara fitowa daga dakuna kallonta. Su Haris ta kira tace su zo su tafi asibiti Maamu babu lafiya. Wadanda ke wurin manya mamakin diramar Gimbi suke yi yayin da ta zamewa yara abin kallo. Tare da Baaba suka sake fita ta shige tasu motar da 'ya'yanta wsu Harisu na gaba suka dauki hanya. ***** Kana shiga dakin Maamu zaka san cewa akwai soyayya da shakuwa tsakanin ma'abota cikinsa. Maamu zuciyarta ta sanyaya har tana ganin ya kamata a sallameta ta karasa jinyar a gida. Ga su Anti Baraka da 'yan uwanta ana ta wasa da zolayar juna. Lokaci lokaci sai ta kalli Awaisu wanda ya kasa dena yawan kallon Rumana. Murmushi tayi domin bai dade da fada mata cewa yana tsoron dasa kiyayyarsa a zuciyarta ba duba da cewa yarinya ce kada abubuwan da suka faru su kasa gogewa a ranta. A lokacin Maamu cewa tayi kada ya damu indai Rumana ce zata hakura. Yanzu ma ganin yadda ciwo yaci karfinta ne yasa ta zama haka har take ganin tamkar laifinta ne na dawowa ita kadai. Da ta fada masa haka cewa yayi yadda ta bashi labarin abubuwan da suka faru a gidansa yasa jikinsa yayi sanyi. Yasan Girmansa ya fadi tana masa kallon wanda ya kasa rike mahaifiyarsa bai cancanci a ga girmansa ba. Maamu gani tayi abin ba komai bane Rumana yarinya ce mai ladabi da hakuri komai zai wuce nan gaba. Amma yadda Awaisu yake ta jan maganar da nuna damuwa yasa tace masa to yasan yadda zaiyi ya dawo da kimarsa a idon Rumana tunda abin ya dame shi haka. Jin ta fadi haka yasa shi saurin mikewa "Maamu ba fa wani abu nake nufi ba abar zancen nan dai". "Dawo dai mu karasa sai ka fada min me kake nufi" Matsar da kujerarsa yayi can gefe cikin 'yan uwansa shi kadai namiji a cikinsu yana dariya. Sai dai duk motsinsa a idon Maamu tana kallon inda idanuwansa suke yawan sauka. Wasu ne suka zo dubiya daga Fika dangin Baban Awaisu maza da mata dakin ya dada kaurewa da hayaniya da gaishe gaishe. Rumana da ta kasance karama duka dakin sai ta matsa can gefe bayan ta gaishesu. Sallamar Babanta taji ta tashi karbar kayan da yake hannunsa idanunta suka sauka akan Gimbi. Nan take jikinta ya hau bari tsoro ya kamata ta kasa motsin kirki a wurin. Awaisu na ganin yadda ta tsorata don bai ma ga Gimbi ba ya taso yazo gabanta ya tsaya tare da rage tsaho ya hura mata iska a fuska. "Umm Ruman are you okay?" Hawaye ne taf ya cika idonta duk yadda ta rinka tsara rashin kunyar da zata yiwa Gimbi ranar da duk suka sake haduwa ji tayi abubuwa da dama sun dawo mata a lokaci guda sai matsanancin tsoro da fargaba. Ledar da ta fara karba a hannun Harisu ya karbe ya ajiye a kasa yace mata ta wuce su fita daga dakin. Daga kan da zaiyi ya mikawa Harisu hannu su gaisa ya hada ido da Gimbi wadda tayi mutuwar tsaye. A zuciye take da yadda ta ga yayiwa Rumana. Harda wani sabon salo wai Umm Ruman. Sunan da rabon da taji ya ambata tum farkon zuwansu Abuja kafin Wangesi ya fara aiki a kansa ita da Maamu ya manta da lamarinsu ballantana sunayensu. Kishi ne ba bala'i a cikin idanuwanta da suka kada sukayi jazur. Me yasa boka yace kada ta biyo mijinta washegari? Me ya faru a kwanaki biyar dinnan da ya dawo Fika? Daga kan gadonta Maamu ta gama kallon komai tsaf ta kuma gano ta inda in sha Allahu zata nunawa Gimbi nata ikon na mahaifiyar Awaisu. Tun da ta fara samun lafiya ita da Baaba Hure suka saka shi a gaba da fada akan sakaci da azkar. Sun karfafa ko ma meye ya same shi da yadda ya damu da neman kudi kawai batare da yawaita yiwa kansa addu'ar neman tsari ba. Yaransa ne suka rungume shi suna murnar ganinsa shima yayi murna domin yayi kewarsu. Gimbi da duk abubuwan da take yi tun zuwanta shawarwarin Ovi ne ta rasa me yake mata dadi saboda ganin da tayiwa Awaisu da Rumana yana nuna damuwarsa a kanta. Kenan asirinta ya soma karyewa tunda har ya damu da wata karan kada miya Rumana. Kula da tayi dakin ita suke kallo yasa ta mayar da idanunta ga Maamu wadda kallo daya yasa ta gane ba karamin ciwo tayi ba. Kanta tayi da gudu har tana takawa Hindu matar Bomai hannu ta fada jikin Maamu tana kuka. "Maamu me ya sameki haka? Ina can ni ban sani ba" Tsigar jikin Maamu har tashi tayi jin rungumar da Gimbi tayi mata. Tsana da kyankyaminta take yi sosai saboda tasan ita ce silar wargajewar farincikinsu. Ba Awaisu da yake da tabbacin ya sanar da ita rashin lafiyar Maamu har tace karya ne ta kara da yiwa su Baaba sharri kowa na dakin da yasan me yake faruwa mamaki ne ya kamashi na wannan karfin hali irin na Gimbi. Da fuska cike da hawaye ta dubi Awaisu ta soma korafin me yasa bai fada mata ba shine ya taho shi kadai don ya sa tayi bakin jini. Wannan abu da take yi duk tuggun Ovi ne da tace mata a haka zata wanke kanta. Ita kuma sukuwa bata san bakin jini Ovi take son kara mata ba yadda asirinta zaiyi saurin tonuwa ta bar gidan Awaisu. Baaba ce tayiwa Rumana alama da hannu akan su fita ita da yaran. Sauran bakin ma duka suka fice don abin ya zama matsalar family. Jikin Awaisu har wani tsuma yake yi saboda bacin rai wai shi Gimbi zata yiwa wannan rainin hankalin a bainar jama'a. Yunkurin karasawa gabanta yayi mata magana yayi Harisu ya girgiza masa kai. Cikin bacin rai ya kaiwa bango naushi zuciyarsa na kuna. Da wace irin mace yake zaune tsahon shekaru sai yanzu halayenta ke bayyana kansu gare shi. Maamu tana kallonsa ga tausayi ya bata taji kwalla ta cika mata ido. Sanin cewa Gimbi bata jin yarensu kuma ita idan ta fada mata da hausa sakon bazai isa yadda take so ba yasa ta yafito Baaba da hannu. Magana tayi mata kasa-kasa yadda sauran bazasu ji ba. Baaba ko dogon nazari batayi ba akan maganar duk da tayi matukar mamaki ta dago ita da Maamu duk suna murmushi "Awaisu jeka wurin Rumananka ka rarrasheta naga ta fita kamar zatayi kuka. Kaima a yadda ranka ya baci dinnan ganinta nasan zai sanyaya maka rai." Anti Baraka da kanenta duka suka bi Baaba da ido cikin rashin fahimtar inda zancen ya dosa. Shi kuwa Awaisu kamar jira yake yi ya fice daga dakin don yasan idan zai cigaba da zama yana kallon Gimbi tana wannan karyar kulawar zai iya kai mata hannu a yadda zuciya ke dibarsa. Fitarsa tayi daidai da zare dukkan wani farinciki da yayi saura a zuciyar Gimbi sai nauyin da taji kirjinta yayi mata. Tsabar takaici ma kasa magana tayi ta rinka kallonsu daya bayan daya. Wai yaje wurin Rumanansa??? Kai kila kunnena baiji daidai ba ta fada a fili ba tare da ta sani ba. Shi kuwa sai da ya kusa isa inda suke tare da su Daula sannan ya tsaya cak yana tunanin me Baaba tace. Rumanansa? Me take nufi da hakan? Daga ido yayi suka hada ido da Rumanan da yake tunani ta dan yi masa murmushin karfin hali a zatonta ko yaji haushin yadda ta nuna tsoron matarsa ne don tasan yana sonta sosai. Shi kuwa wannan murmushin jinsa yayi tamkar an *kunna fitila* a cikin zuciyarsa har abin ya bashi tsoro. Rumana ce fa 'yarsa. A cikin sakin kuma cikin yarensu Anti Ummukulsum ta tambayi Baaba me take nufi da Rumanan Awaisu. Nan tayi bata bayanin sunyi ne kawai don bata ran matarsa. Maamu ta kafe Harisu da ido tace "ni ba da wasa nake yi ba dana ka taimakeni ka kara yi min wannan alfarmar" Baaba tayi saurin kallonta "Da gaske kike yi Awaisu kike son hadawa da Rumana?" "Ba don na huce takaici ko bacin ran da matarsa ta saka min ba kawai na kula kamar shima yana son hakan" A raunane take maganar ta rike Baaba Hure "kiyi hakuri idan na bata miki rai, ban ko yi tunani ba" Baaba tace "da gaske kina son wannan hadin?" Su Harisu duk suka zaro ido jin wannan maganar ta iyayensu. Maamu na cewa eh Baaba tace "In sha Allahu anyi an gama alfarmar Manzon Allah SAW" Dakin tsit yayi su Harisu an ma rasa me cewa komai. Gimbi tana tsaye suna yare bata fahimci komai ba sai dai zuciyarta ta bata akwai abin da suke kullawa jin an ambaci sunan Rumana da na mijinta. Wani zafi ta fara ji a jikinta tun daga tsakiyar kai har tafin kafa. [15/08, 17:46] ‪+234 803 272 5896‬: *KASHE FITILA*💡35 *Batul Mamman*💖 Babu wanda ya kula ta sai ma Harisu da ya fita don ya rasa abin cewa. Awaisu ya hango ya kusa karasawa inda su Rumana suke yayi saurin binsa ya tare shi. Rasa abin fada yayi don jin wannan hadi da bai taba tsammani yayi ba daga sama. Sai kuma ya daidaita kansa yace ya kamata yaran suci abinci a mayar dasu gida saboda sun sha hanya, gashi suna isowa an sake tahowa dasu asibiti. Awaisu yayi na'am da shawarar "ni zan zauna a nan waje har su gama don raina bazai jurewa karairayin Gimbi ba" Kafadarsa Harisu ya dafa "kayi hakuri Awaisu ni bana son wata rigima ta tashi a asibitin nan ba mutumcinmu bane. Duk abin da zamuyi ka bari a koma gida" Daga nan Rumana ya kira ya umarceta da zubawa su Amir abinci. A dan tsorace ta shiga dakin kai a kasa taki bari su hada ido da Gimbi wadda take sankame a gefe guda zuciyarta tana ruri kamar ana hura mata wutar bacin rai. Ganin Rumanan sai ta dan saita kanta ta rungumota. Tamkar mazari jikin Rumana ya hau bari saboda tsabar tsoro. "Oyoyo Rumana kin tafi kin barni da kewa ganin Maamu yasa ban kula babbar 'yar Mummy ba." Yawu ma kafewa Rumana yayi ta kasa daga harshe tayi magana sai murmushin yake. Gimbi na kula da yadda ta tsure a ranta taji dadi yarinyar nan bata isa ta kawo mata raini ba don ta riga ta dasa mata dafi a zuciya. Hannunta ta kama tayi hanyar fita daga dakin da ita tana dariya "Shine kika biyewa Abbanku baku fada min Maamu babu lafiya ba ko? Muje waje dai musa labule akwai labari" Rumana ido yayi kwal-kwal da hawaye ta juyo neman agaji wurin iyayenta tana so wani cikinsu ya hana Gimbi fita da ita daga dakin. Anti Suwaiba ce tayi yunkurin tashi ta hana Baaba ta girgiza kai. Bayan fitarsu ganin cewa akwai su Haris a dakin ta sake magana da yarensu "Ku kyaleta hakan da tayi ya tabbatar min tayi zargin wani abu game da maganganun da mukayi dazu. Ga dukkan alamu tsorata ta zata yi." "Kuma shine zaki hana a tsayar da ita? Kada ta cutar da Rumana" cewar Maamu tana sako kafarta kasa daga kan gadon. Baaba ko a jikinta harda dariya tace "nafi so ta cigaba da tunanin tayi nasara wannan ne zaifi kona mata rai idan taji an shafa fatiha" Abinci ta zubawa yaran da kanta tace su ci a kama hanyar komawa Fika su huta. Su Maamu duka hankalinsu a tashe tace kada su damu da kanta zata fita ta dawo da ita. Tafi so dai ta bata damar da zata ji kamar babu wanda ya isa sai ita kadai. Wani dan wuri da babu kowa Gimbi ta kai Rumana ta sakar mata hannu tare da hade fuska sosai "Rumana kin fadawa su Abban Haris wani abu ne?" Hadiyar yawu tayi da kyar "Mummy wane abu?" "Au har kin manta na fada miki ni ba Mummynki bace? Da kika dawo gidan ubanki baki hadu da taki uwar ba?" Bata ce komai ba hakan ya kara tunzura Gimbi amma dole ta daure tana wurin da dolenta tayi a hankali saboda 'yan uwan Awaisu ne ko ta ina. Zaro idanu tayi tana mata kallon banza "Akwai wani abu tsakaninki da Abban Haris? Naji ana ce miki Rumanansa" Wannan karon ma kasa magana tayi sai ma tsoro da taji ya mamayeta tunda bata nan lokacin da Baaba ta fadi hakan. Ta gama kidemewa karshe kamar daga sama taji muryar Awaisu ya kirata cikin sanyin muryar da ko kadan batayi kama da muryar da uba zai kira 'yarsa ba. Ita kanta Rumana ba don rashin sabo ba da ta dago cewa Uncle Awaisu fa wani salon shagwaba yayi mata. "Umm Ruman kije ki gani idan sun gama cin abinci ku fito mu tafi dare yana yi kuma nima yunwar nake ji baki bani abinci ba" Tirkashi, zuciyar Gimbi ta kumbura suntum da bacin rai mara misaltuwa. Kallon Rumana tayi wadda ta kara shiga cikin duhu saboda rashin fahimtar meyasa yayi magana irin haka. Ita ina ruwanta da cin abincinsa? Ko da can ma ai ba ita take bashi ba. Yadda ya tsareta da kallo yasa ta cewa "bari na duba idan akwai saura sai na zuba maka" Kamar zata bi iska don sauri haka ta bar wurin. Bayanta yabi da kallo kuma yasan tabbas Gimbi shi take kallo yayi dan murmushi yayi gaba yana jin yadda take kiransa hankali a tashe. Sai da ya koma wurin Harisu yake fada masa me yaji Gimbi na tambayar Rumana. Dama tare suka hango fitowarsu Awaisu yayi saurin tahowa don yasan bazaa kulla alkhairi ba. Ita kuwa Gimbi da zaa aunata a lokacin tabbas jininta ya hau. Ta rasa gane meye yake faruwa. Tunda tazo fa ko kalma daya bata shiga tsakaninta da Awaisu ba. Abubuwa ke neman rikecewa ta zaro wayarta daga jaka ta kira Ovi. Kuka ne ya taho mata ta danne don kada wani ya fito ya ganta ta zayyana mata halin da take ciki. "Ovi please kije wurin Boka ki sanar dashi. Idan abubuwa suka cigaba a haka ina kyautata zaton komai zai lalace zuwa matakin da bazaa iya gyarawa ba." Ovi ta gimtse dariyarta tace "ki turo kudi yanzun nan zan tafi wurinsa. Ina muka ga ta zama ana neman bata shirin da aka jima ana yi. Dayan maganin nan dai da ya baki kiyi kokari ko ta wane hali ki shafawa maman tasa. Boka yace da kanta zata ce ya biyoki ku tafi kuma bata son kara ganinsa. Kinga daga nan kin huta" Gimbi ta sauke ajiyar zuciya sai dai tana kokontan yadda zata iya shafawa Maamu magani babu wanda ya kula. Ta kula wani kallon tsana suke yi mata shiyasa take tunanin ko Rumana tazo ta fada musu irin zaman da sukayi. Sai kuma ta ga babu dalilin damuwa saboda idan boka yayi mata aiki a kansu babu wani wanda ya isa ya daga mata yatsa. A take ta turawa Ovi dubu hamsin sai dai tana jin faduwar gaba game da maganar Baaba Hure akan kiran Rumana ta Awaisu. Tana nan tsaye suka fito tare da su Anti Baraka yau Anti Ummukulsum ce zata kwana. Babu wanda ya kulata taji jikinta ya danyi sanyi. Dakin ta koma tayiwa Maamu sallama harda alkawarin gobe da wuri zata zo don ita zata kwana da ita ma ta fita. Motar Awaisu ta nufa domin tana son magana dashi akan abubuwan da ta gani daga zuwanta. Sai da Baaba Hure ta tabbatar nan ta taho har tana cewa su Haris su tafi motar da suka zo da ita kawai Baaba tace "Rumana kin gaji ne haka kike tafiya da kyar? Awaisu bude mata gaba ta zauna kannenta sai su zauna a baya ku fara yin gaba" Murmushi yayi ya bude kofar yana satar kallon yadda Gimbi ta kame kam a wurin tana kallon ikon Allah. Rumana itama tsayuwa tayi zata waiga ta ga yaya Gimbi tayi don tayi tunanin tare zasu tafi da Awaisu taji yace "Shiga mana ko sai na dauke ki ne?" Kunya taji tayi saurin shigewa yana yi mata dariya. Baaba Hure a zuci tace karen bana maganin zomon bana Awaisu kayi min daidai. Taji dadi da ta lura da yadda kalar fuskar Gimbi ta canja gabadaya. Harisu dama ya riga ya tayar da tasa motar su Anti Suwaiba sun shiga. Baaba Hure suke jira ta tsaya ta karewa Gimbi kallo "Kun zo mota a cike zaki koma ke kadai. Ko na dawo taku motar ne na tayaki hira?" Duk yadda taso daurewa bata san sanda ta watsawa Baaba harara ba sannan tayi gaba kamar zata tayar da kura. Baaba tana dariya ta karasa motar Harisu suka tafi. Shima Awaisu jan tasa yayi yaransa suna ta yi masa hira yana amsawa cikin nishadi. Rumana kuwa shiru tayi jikinta ya kara mutuwa. Me zaisa ace ta shiga motarsa ga matarsa a wurin da ta gama bata tsoro dazu. Gimbi na shiga mota sai hawaye ya balle mata. Tsawa ta dakawa dreban akan ya fita daga motar. Jiki na rawa ya fita tana kuka ta kira uwargijiyarta Ovi ta fada mata sabon lamarin da yake faruwa. "Ovi cikin kankanin lokaci daga zuwana mutanen nan zasu kasheni da bacin rai. Ki fadawa Boka ko wane irin shiri suke yi ya wargaza zan bashi ko me ya bukata" Kwantar mata da hankali Ovi tayi da kyakkyawan alkawarin cewa daga gobe idan taso duka gidan sai ta juyasu suga tsiya. Tayi wani mugun murmushin auno yadda zata fanshe bacin ran da Awaisu ya saka mata. ***** Har gari ya waye bata ga Awaisu ba domin jiya sun rigasu isa Fika. Da suka iso kuma bata ma ga motarsa ba. Daki aka bata ta shiga tana tabe baki. Ta tsani zuwa garin nan domin a takure take jin kanta. Su Haris sun bi 'yan uwansu maza yaran Harisu a dakinsu suka kwana. Daula uwar iyayi ma wurin Rumana ta zabi kwana suka bar Gimbi ita kadai. Da aka bata abincin dare cewa tayi bata ci saboda tunani yayi mata yawa. Shiyasa da safe Anti Amarya taki aika mata da breakfast. Shiru Gimbi na jiran abinci don ba karamar yunwa take ji ba taji shiru sai hayaniyar yara. Nata 'ya'yan da take ji kamar 'ya'yan gwal babu wanda ya leko dakin. Takaici ya sake kamata. Sai wurin karfe goma Awaisu ya shigo gaishe da Baaba kafin ya wuce asibiti. Bayan sun gaisa yana cin abinci tasa aka kira mata Harisu. Nutsuwa sukayi a gabanta tace tana fatan sun amince da maganar da akayi jiya na auren Rumana. Awaisu ya dago kai da sauri "Aure kuma Baaba karatunta fa? Saura watanni ta gama secondary. Daga dawowarta ko wata biyar bata yi ba ta sami miji ne?" Sai a lokacin ta tuna baya dakin suka yi magana a asibiti. "Aure ne zaa hadaku Awaisu ina fata bazaka watsa mana kasa a ido ba" Harisu yayi saurin kallo shi kuma ya kawar da nasa kan saboda har yanzu bai san yadda zai kwatanta yaya ransa ya karbi wannan hadi ba. Baaba Hure ta lura dasu tayi murmushi "wannan hadi wanda bamu taba kawowa ko da wasa zamuyi shi ba ina so ku dauke shi a matsayin rubutaccen al'amari. Bansan me Maamu ta gani ba amma ni dai tunda ta fada zuciyata ta aminta ta kuma sami nutsuwa sosai akan hakan. Ina so a matsayinku na 'yan uwa kuyi shawara da juna. Idan har wannan hadin zai taba muku zumunci kafin mu tafi asibiti yau ku yanke shawara ku fada min." Babu wanda yayi magana a cikinsu Baaba Hure ta tashi ta fita. Sai suka koma yiwa juna kallon kallo. Awaisu kunyar Harisu yaji ta rufe shi. Shi da kansa yana mamaki tun zuwansa Fika yake yiwa Rumana kallo na daban. Yarinyar da aka haifa a gabansa har ya saka mata suna. Wannan abu da kunya sai dai ya rasa gane dalilin da yasa shima zuciyarsa take kwadaita masa da ya amince. Harisu ya gyara zama yana kallonsa "nasan yadda nayi mamakin wannan magana kaima kayi. Ina so nace ban yarda ba domin Rumana 'yarka ce amma bazan taba yiwa iyayenmu musu. Abu daya zan tambayeka dan uwana....ka amince da auren nan da zuciya daya?" Ya Ilahi sosai Awaisu yaji kunya musamman ganin yanayin Harisu ba yadda ya saba ba. Yasan ko shine zaiji kwatankwacin haka ko ma fi. Bai taba tunanin faruwar haka ba amma shima tasa zuciyar ingiza shi take yi akan kada ya cuci kansa. Kansa ya sunkuyar "Yaya Harisu... " sai kuma yayi shiru saboda nauyin amsar da zai bayar. Tashi Harisu yayi batare da ya saurari amsar tasa ba ya fita. Bai dade ba suka dawo da Baaba a gabanta yace ya amince. Awaisu ya kasa kallonsu duka su biyun saboda tsananin nauyi da yaji. Harisu yasan cewa duka su biyun abin yazo musu a bazata kuma baya ganin laifin kanin nasa sai dai har ga Allah yana tausayin Rumana. Nasiha sosai Baaba tayi musu akan zumunci da fatan wannan hadi ya zame musu alkhairi mai dorewa. Awaisu ne ya fara fita Baaba ta cigaba da yiwa Harisu nasiha don tasan sai a hankali zai nutsu da maganar. Ba kuma don baya son Awaisu ba sai dai ko waye yaji zaiyi mamaki duba da alakar dake tsakaninsu. Ranar Gimbi kirikiri taki zuwa asibiti wai bata da lafiya saboda Ovi bata kira ba. Abinci kuwa sai da rana ta take Anti Amarya ta aika mata. Ba don gudun batawa Harisu rai ba ma ai so tayi ta gasa ta yadda ta yiwa Maamu. Da Maamu taji sun amince duka su biyun tayi ta saka musu albarka shi da Harisu. Sai kuma ta bawa Awaisu shawarar ya koma bakin aikinsa tunda suna sa ran nan kwana biyu a sallameta. Dr. Yana taji dadin yadda Maamu take samu sauki sosai idan ta gama round har hira take zuwa suyi. Washegari Gimbi ta sami kuzarin zuwa asibitin saboda Ovi ta kirata ta fada mata Boka ya kwana aiki akan Awaisu da duk wani wanda zai iya kawo mata cikas. Yaranta tun safe suka bi 'yan uwansu da Abba ya cika a mota suka tafi. Rumana da yayyenta dake gidajen mazajensu suka tafi har yanzu ita da iyayenta mata babu wanda yake da masaniya akan hadin aurenta da Awaisu. Hayaniya sosai suke yi a dakin Maamu kuma da ita ake hirar wani likita yazo yace ko su rage murya ko su fita. Harisu yace gara su zo su tafi kawai don hayaniyar tayi yawa. Yaran aka fara turawa suka tafi Rumana zata bisu Baaba tace ta zauna sai tabi Awaisu. Duk da tayi mamaki haka dai ta zauna. Yayyenta basu kawo komai ba suka fita. Dakin ya rage Gimbi, Baaba da 'ya'yanta duka su hudun da Awaisu. Hirarsu suke yi babu wanda ya sakata ga Maamu tana ta jan Rumana da hira tana biye mata suna dariya. Gimbi ta auna taga wulakancin yayi mata yawa kuma dai an tabbatar mata Boka ya gama dasu. Awaisu ta kalla tana wani kada kai tace "Abban Haris ya kamata mu fara shirin komawa Abuja ko" A dakile ya amsa mata "tare muka zo?" Baaba tace ya kamata ya koma saboda aikinsa. Maamu ma tace dama tayi masa maganar jiya. A wautar Gimbi da mika wuya ga boka sai tayi tsammanin aiki ne ya soma ci shiyasa abin da ta fada duka suka bada goyon baya. Tayi shu'umin murmushin nasara sannan ta kada kai ta kalli Harisu. "Yaya Harisu ranar da nazo na taho muku da kayan abinci amma da kai da matanka babu wanda ya nuna ya gani bare ayi godiya. Ko ba komai nasan na rage maka wani nauyin" Baki bude suka bita da kallon mamakin wannan furucin nata. Awaisu yaji ya mugun tsanar kansa da ya rasa matar aure sai Gimbi. Kafin yayi magana Anti Suwaiba rai a bace tace "uban waye ya rokeki da har kike jiran godiya. Ke Gimbi! bari kiji in fada miki wallahi baki da arzikin da zaki kawowa iyayenmu abinci" Baaba tace cikin bacin rai "Suwaiba bana son sakarci ki wuce ku tafi kawai ki kyaleta" Dayake dama itama bata iya fushi ba sai ta kasa yin shiru "Baaba wallahi shirun da ake yi mata ne yasa take tunanin ana jin tsoronta. Bayan kin kusa kashe Maamu da yunwa a gidanki shine don rashin kunya zaki zo ki taho da kayan abinci? Billahilzi Gimbiya idan zaki koma baki kwashe kayan nan ba sai na nuna miki ke karamar mara kunya ce. Ki dubemu da kyau gabadayanmu babu matsiyaci balle kice maula muke yi." Gimbi ta rasa abin yi jin wannan magana ta tabbatar asirinta yana daf da tonuwa sai kawai tasa kukan munafirci "Yaya Suwaiba me yayi zafi haka" "Munafuka kada ki sake kirana Yaya. Da can kina kiran sunayenmu ne ma, sai yanzu don gulma tunda kika zo kike cewa kowa yaya" Anti Baraka ta kama hannun Suwaiba tace tazo su fita daga dakin ta kwace. Ana ta yi mata magana amma ranta ya gama baci taki sauraron kowa "Ku barni na amayar mata da abinda ke raina. Gara ta sake shiri idan tana tunanin tayi nasara ne. " Jikin gadon Maamu ta karasa ta dafa ta "dubi yadda kika mayar mana da uwa. Ba don tsahon kwana ba da tuni bakinciki da ciwukan da kika kwasa mata sunyi ajalinta " Rumana gani tayi dakin ya kaure Gimbi na kuka ana ta kokarin Anti Suwaiba tayi shiru taki sai ta tashi ta fita tana kuka. Awaisu na ganin haka baiyi tunanin komai ba ya bi bayanta yana kiranta saboda yadda ganin hawayenta ya tayar masa da hankali. Kukan karyar Gimbi ta dena ta bisu da kallo tana son gano ainihin me yake faruwa dasu biyun. Harisu da kansa yaja hannun Suwaiba tana ta fada yayi waje da ita sauran yan uwansu suka biyo bayansu. Baaba takaici ya isheta ta cewa Maamu bari taje ta tabbatar duka sun tafi yau ita zata kwana. Tana fita Gimbi tabi bayanta sai ta tuna da maganin da aka bata. Lekawa tayi ta kallo hagu da dama ta tabbatar babu idon sani sannan ta dawo ta rufe kofar. Fitowar Baaba da leken da Gimbi tayi akan idon Dr. Yana wanda fuskar Gimbi ta kasance bakuwa a gareta. Saurin barin matar da take yiwa kwatancen dakin hoton kashi tayi ta taho dakin Maamu da sauri saboda alamun rashin gaskiya da ta gani a jikin mai leken. Tana bude kofar ta ga Maamu a tsaye tana matsawa baya ga Gimbi rike da wani abu kamar izgar doki tayi kanta tana kokarin shafa mata. Cikin zafin nama Dr. Yana tayi kantza.....[15/08, 17:45] ‪+234 803 272 5896‬: *KASHE FITILA*💡36 *Batul Mamman*💖 Gimbi bata ankara ba taji an damki hannunta ana kokarin kwace abin da take niyar shafawa Maamu. Damkewa tayi iya karfinta ta dage ta ture Dr. Yana sannan ta boye abin da sauri. Mikewa Dr. Yana tayi ta tafi ta riko Maamu wadda ta gama tsorata jikinta sai rawa yake yi. Kirikiri Gimbi ta nufota da abin har tana fadin wasu kalmomi da bata gane ba. A tsorace tace da Dr. Yana ta fitar da ita daga dakin gida zata tafi. Duk yadda Dr. taso kwantar mata da hankali tace ita dai fita zatayi kawai. Saboda jikinta bai gama kwari ba dafata tayi suka fito waje tana cewa su Harisu suna nan wajen suyi sauri kafin su tafi. A bakin mota suke tsaye Baaba sai fada take yiwa Anti Suwaiba. Awaisu da ya rasa inda Rumana tayi ya hango Maamu da Dr. Yana ya nufo su yana tunanin me ya fito dasu. Kafin ya karaso sun kusa zuwa wurin motar Harisu. Gimbi suka gani ta taho cikin mugun sauri har tana haki kafin duka suyi magana ta iso tare da yiwa Dr. Yana kallon banza. "Ke wace irin likita ce zaki shigo daki haka kawai ki fitar da mara lafiya batare da wani bayani ba?" Su Harisu sanin halin Dr. Yana sai suka fara tunanin ko wani salon shiga rigimar nata ne. Gimbi ta cigaba da magana tana kallon Maamu da tausayawa "Maamu kinji tsoro ko? Ai in fada muku kuna fita wani abu ne ya shigo mana a guje na kasa ganewa ma bera ne ko mage. Shine na samo abu zan kore shi ganin Maamu ta tsorata kawai sai wannan matar ta shigo ta fito da ita. " "La ilaha illallah muhammadur rasulullah sallallahu alaihi wa sallam" Dr. Yana ta fada tana tafa hannuwa saboda tsabar mamakin wannan matar. Kallonsu tayi duk sun zuba mata ido ta fada musu abin da ta ga Gimbi tana shirin yi a dakin. Gimbi ta dafe kirji rai a bace "anya kina da hankali kuwa, uwarmijina ce fa kike cewa zan shafa mata wani abu. To a chajeni idan kun yarda da abin da take fada. Maamu fada musu gaskiya" Wani irin kallo Maamu ta yiwa Gimbi wanda ya tsorata ta sannan ta kada kai ta bude mota ta shige ta zauna. Gimbi ba karamar makira bace. Gara su tafi gida kawai ayi wadda za'ayi gudun kada suyi abin fadi a asibitin. Baaba tace "likita mungode miki bari mu tafi da ita kawai tunda dama gobe ne sallama." Dr. Yana tace "ku tsaya kawai Baaba bari na kira security yaje ofishin 'yab sanda mafi kusa yayi report. Ni nafi so ayi komai a gama yanzu. In ga abu da idona mata ta nemi raina min hankali" Tsoro karara ne ya bayyana a fuskar Gimbi kada ayi binciken da gaske yasa ta fara masifa baji ba gani tana cewa itama gida zata tafi ta fuskanci basuyi maraba da zuwanta ba shiyasa suke yi mata haka gashi abin ya hada da zargi kuma. Dreban da ya kawota ta kira yazo ta shige mota ko waige babu don tsoron kada a nemi ta fito ma suka tafi rai a bace wannan shegiyar likita ta cuceta domin damarta ta karshe kenan wurin amfani da wannan maganin kuma ta rasa. Tana tafiya Dr. Yana tace ya kamata wani cikinsu ya tsaya karbar magungunan Maamu da takardar sallama sannan ta kara jaddada musu lallai a binciki Gimbi ba karya take ba. Awaisu yace to su tafi zaije yayi settling komai. Su Baaba duka motar Harisu suka shiga suna al'ajabin halin Gimbi. Anti Baraka ce ta leko ta taga tace ko dai ta fito ne ta taya shi hada kayan da suka baro a dakin. "Ki barshi kawai Rumana sai ta hada kafin na gama da wurin karbar maganin" Dariya matan suka soma yi masa harda zolaya sannan suka tafi. Dr. Yana ya tsayar yanayin fuskarsa babu alamun wasa yace ta fada masa abin da ta gani. Tana fada masa yanayin fuskarsa ya sauya zuwa bacin rai sosai yace idan babu damuwa yana bukatar numbarta saboda zai yiwu ya nemeta shaida. Kafin ya gama magana ma ta fada masa numbar. Katinsa ya zaro ya mika mata sannan yace zai fara zuwa dakin ya duba ko Rumana ta koma don bai ganta a waje ba. Yana zuwa kofar dakin suka kusa karo da ita ta fito da gudu. Ganin Awaisu yasa ta dan dakata amma hankalinta a tashe yake "Uncle ban ga su Maamu ba kowa ya tafi" Dan sakin fuska yayi saboda ganinta kawai yaji ransa ya soma sanyi. "An sallameta ne yanzu suka tafi." "Sallama kuma Uncle ba ance sai gobe ba. Ko wani abu ya sameta ne?" Ta fada ido yana kawo ruwa gabanta na tsananta bugu. Rage tsaho yayi ya kura mata ido ba shiri taja baya ganin ya matso da fuskarsa kusa da tata. "Maamu lafiyarta kalau. Ki hada kayan kafin naje nayi settling bills sai mu tafi" Bata san lokacin da tace "mu kadai?" "Eh mana, Uncle da Umm Rumanansa" Baki ta bude jin me yace shi kuwa ya juya ya fita. Ita fa ta kasa gane meyasa yake yi mata magana yanzu a wani irin yanayi daban ba yadda ta saba ba. Duk da ita take ce masa Uncle Awaisun Rumana a da yanzu idan ya fada kunya ma take ji. Kusan minti talatin yayi kafin ya dawo suka kwashe kayan suka kai mota. Dr Yana har bakin motar ta rakasu sukayi sallama da Rumana. Sun fara tafiya shiru sai lokaci lokaci da ta kula yana yawan kallonta. Ta rasa me yake damun Uncle Awaisu yan kwanakin nan. Katse shirun yayi ta hanyar yi mata tambaya. "Saura sati nawa ku koma school?" "Bai kai sati biyu ba" "Yayi kyau ana komawa sai SSCE ko" Ta gyada kai fuskarta na nuni da farincikinta. "Idan kika gama zaki yarda ki dawo Abuja?" Da saurinta tace "Allah Ya kiyaye" Awaisu yayi murmushi. Ai dole ta tsani Abuja to kuma gashi a nan yake aiki "Ba kya son zama dani ne?" Ta hau girgiza hannu "A'a ina so mana, amma dai ...." "na gane kada ki damu aure zan kara sai ki zauna da amarya" Murna yaga tayi sosai harda juyawa ta fuskance shi da kyau "Allah Uncle, ashe zamu sha biki" "Sai na fadawa Gimbi kina murna zaayi mata kishiya" Gimtse dariyarta tayi ta sunkuyar da kai tana yi kasa kasa. Allah Ya kara tace a zuci har taji tana kwadayin zama a gidan ko na kwana daya ne ta ga Gimbi da kishiya. "kema ance tunda kika dawo kike ta tara samari. Kuma wanda ya fada min bazai miki karya ba" A raunane tace "ayya Uncle dan abokin Baba ne na bayan gida kuma nace bana so. Sai wani malamin English a makaranta sannan yayan wata yar ajinmu. Duka fa nace bana sonsu" Hannu daya ta ga ya saka ya danne kirjinsa bangaren hagu yace "wayyo zuciyata" A rikice tace "yi parking a gefe Uncle me ya sameka? Ina wayarka na kira Baba" Kashe mata ido yayi yana dariya "kishi ne dama kuma ya koma tunda naga an damu dani" Matsawa tayi kunya ta rufeta bata san lokacin da tace "wai Uncle sai ya rinka yi min abu kamar budurwa da saurayi" Dariyarsa ce ta tabbatar mata da cewa yaji me tace ba shiri ta rufe fuskarta da mayafinta ta shiga kogin tunanin chanjawar Uncle Awaisu. A hankali yaji numfashinta ya sauya jikinta ya dan saki. Mayafin ya ja a hankali ya bude mata fuska ya ga ashe bacci ne ya dauketa. A daidai wannan lokacin yaji wata irin soyayyar Rumana ta shiga ransa. Tabbas da farko yaji ransa ya kwadaita masa amsarta a matsayin mata kuma komai tayi yanzu yana burge shi. Amma a yanzun nan da ya kalleta soyayya ce ta kamshi wadda ta bashi mamaki shi kansa. Rumana bata cikin jerin matan da ko a mafarki ya taba tunanin wani abu makamancin wannan zai shiga tsakaninsu. Allah mai iko. Mutane biyun da Gimbi ta sanya masa fita harkarsu ya manta da lamuransu sune a yanzu cikin dan kankanin lokaci yake jin zai iya komai indai bai sabawa shariah ba domin ya faranta musu. Har gama parking bata farka ba kuma dole ya tasheta don har kannenta sun fito daukar kaya daga motar. Rasa yadda zaiyi ya tasheta yayi sai yayu saa Daula ta fito yace ta tasheta su shiga ciki. Ranar har dare yayunsu mata suna gidan ana shawara game da matakin da zasu dauka akan Gimbi. Maamu ta tabbatar musu da zancen Dr. Yana gaskiya ne tace tana rokon alfarmar su gaggauta hukunta Gimbi kafin ta bar Fika. A lokacin Awaisu ya kira Alh Maitama ya roke shi akan ya fada masa idan abin da yake son fada ya dangan ci asiri da Gimbi da Anti Bebi sukayi. Alh Maitama bai boye masa komai ba har yadda aurensa da na 'yarsa ya mutu. Ya tausaya musu sosai kuma ya sanar da su Baaba yadda suka yi. ****** Kamar sun san haka zata faru dama tun jiya Harisu da Awaisu sun sanar da kawun nansu na kusa batun hada aure da Rumana. Duk da sunyi mamaki amma kowa ya basu hadin kai a ganinsu hadi ne na kara dankon zumunci a tsakaninsu. Shiyasa tun wurin karfe tara na safe Harisu ya tura Abba ya sanar dasu dalili yasa dole a daura auren nan a yau bayan sallar Juma'a. Shi kanshi Abba da aka aika yayi mamaki matuka. A cikin gidan kuma tun daren Harisu ya sanar da matansa. Mama da Anti Amarya murna sukayi sosai. Maman Rumana kuwa ta kasa magana har suka fita daga dakin da yake girkinta ne. Kuka ta sawa Harisu tace tana tsoron kada Gimbi ta sabauta mata 'ya. Kusan kwana yayi yana rarrashinta da ban baki. Shima akwai wannan tsoron a ransa amma shawara ce da iyaye kuma yasan ko da aure ko babu Awaisu mai rike masa iyali ne bisa amana ba don ya hadu da hatsabibiya Gimbi ba wadda bata san wainar da ake toyawa ba. Tun da ta dawo daki ta shige ta hada kayanta da zummar zata bar garin da safe. Ganin basuyi mata maganar abin da tayiwa Maamu ba yasa tayi tunanin wayar da tayiwa Ovi daga can bangaren boka ya rufe musu baki kamar yadda ta bukata Ita kuwa Rumana bata san me akeyi ba don kitso ma tayi tafiyarta makota. ***** Duka iyalin gidan tun daga kan su Baaba, Harisu da matansa, su Anti Baraka, Awaisu da Gimbi ne zaune a falon Harisu na karbar baki. Da Awaisu ya hana Gimbi tafiya yace ta jira zasuyi magana bayan masallaci bata yi tsammanin haka zata shigo ta tarar da wurin a cike ba. Gabanta ne ya fadi sosai ta sami wuri ta zauna a can gefe. Kawun nansu da suka shaidi daurin auren Rumana da Awaisu a masallacin Juma'a duka Harisu ya sallamesu akan cewa sai washegari zai sanar da jama'a ayi walima a kofar gida. Yau suna da abu mai mahimmanci da zasuyi shi da Awaisun. To gasu duka a falon Baaba ce ta soma magana tana kallon Gimbi ido cikin ido.. "Ba tare da dogon zance ba Gimbiya wannan zaman naki ne. Bisa amana mijinki ya dauki mahaifiyarsa da 'yar dan uwansa ya kai gidanki kin nemi halaka su. Bansan me zuciyarki ta ayyana miki ba a lokacin da kike azabtar da surukarki da yunwa. Babu ci babu sha sannan kin hana dan cikinta shiga lamarinta " Mikewa Gimbi tayi a fusace saboda indai ba borin kunya ba zatayi asirinta ya riga ya gama tonuwa. "Awaisu kana ji kana gani yadda 'yan uwanka suka saka ni a gaba da sharri tun da na sa kafa a garin nan. To wallahi ni bazan yarda ba ai nima ina da gata ba daga sama na fado ba." Da yake yana kusa da ita wani wawan duka ya kaiwa bakin a take ya fashe sai ga jini. Baaba kuwa ta hau shi da fada tace ya tashi daga inda yake. Bayan ya matsa ya kalleta cikin bacin rai "Gimbi kin cutar dani kin sanya mahaifiyata zubar da hawaye a dalilin juya mata baya da nayi" Idonta da hawaye tace "kada ka yarda sharri suke son yi min" "Nafi kowa sanin halinki Gimbi. A lokuta da dama sai kiyi abu raina ya baci sosai amma na rasa dalilin da yasa ko kallon banza bana iya yi miki. Allah sai Ya saka min gwargwadon hawayen da mahaifiyata ta zubar saboda bakinciki. Kuma ki sani yadda kika yi abin da kike so a lokacin da kike so nima yanzu lokacina ne. Gimbi sai na soya miki gyada a hannu kinyi nadamar aurena" A gabansu ta dauko waya zata kira Ovi saboda tashin hankalin da ta shiga na maganganun Awaisu. Haka 'yan uwansa kaf suka ci mata mutumci tasha Allah Ya isa babu iyaka akan halin da tasa Maamu. Tunawa tayi da inda take ta fasa kiran wayar amma ranta ya kololuwar baci. Idanunta jazur tana kumfar baka tace "Awaisu idan ka cika dan halak ka sakeni. Meye a cikin auren naka wanda bazan iya samu ba idan na auri wani?" Murmushinsa da take masifar so a da yayi mata "aure ni dake yanzu muka fara. Yanzu dai ki tsaya a kawo miki amarya ki karbi amana. Idan kuma kinfi so ku hadu a Abuja babu damuwa" Komai na jikinta ne ya tsaya a lokacin da ya ambaci amarya. Jikinta na rawa tace "aure kayi Awaisu? Ni zaka wulakanta kayiwa kishiya. Wace shegiyar ce take jin zata iya zaman kishi dani?" Magana take kamar zata zare ransu fes duka da ganin ko babu komai sun soma ramawa. Maamu ce tace "kada ki sake zagar mana 'ya" "Auuuu wani munafukin ne yazo ya bashi 'ya ya aura? To mu zuba ni daku wallahi baa isa a daura auren ba idan har ina numfashi" Su Anti Baraka sai dariya Gimbi ji take kamar tayi hauka don takaici. Ledar goro Anti Suwaiba ta jefa mata "Yau dai bokanki yayi karya domin an riga an shafa Fatiha tun dazu. Awaisu ya zama angon Rumana" "Jakar uba, Rumana??? Rumana fa kika ce?" Kafin su ankara tayi kan Awaisu a gigice zata kaiwa wuyansa shaka. [15/08, 17:45] ‪+234 803 272 5896‬: *KASHE FITILA*💡37 *Batul Mamman*💖 Fincikota taji anyi ta juya a fusace ta ga waye ya rikota taji saukar mari. Anti Baraka ce da wannan aikin halin Gimbi ya kaita makura duk da kasancewarta mafi hakuri a cikin 'yan uwanta. Kumatunta ta rike don ba karamin shigarta yayi ba kalli Awaisu dake tsaye ya rasa yadda zaiyi. Kunyar ace matarsa ke wannan aika-aikar da bacin ne suka cika zuciyarsa. Idanunta babu hawaye ko kadan tunda shima kuka wuri yake samu "Abban Haris yanzu ka yarda da abin da nake fada maka ko? Mutanen nan sam basa kaunarka shine saboda sun rasa yadda zasuyi su rinka tatsarka suka hadaka da Rumana....wai Rumana yarinyar da ba haihuwarta ba uwarta ma a kan idonka aka aurota." "Gimbi kada ki kure hakurina wallahi. Ban taba sanin cewa akwai ranar da zanyi nadamar watsawa Yaya Harisu kasa a ido a lokacin da ya nema min matar aure na bijire ba sai yanzu." Cewar Awaisu yana daga murya. "Dama har wata matar ya taba sama maka? Hasashena bai zama kuskure ba da nace kudinka suke nema. Wato yaso baka wadda zata rinka sata ta kawo maka" Hannu ya kai zai daki ko ma ina ya samu a jikinta Harisu ya rike "Awaisu kada kayi abin da nan gaba zakayi dana sani. Ka tuna akwai rabo a tsakaninku bai dace ka daketa ba" Har wani huci yake yi ya dubeta tana kallon kowa daidai "ki tashi ki kama hanya ki koma Abuja ki jira sauran abin da zai biyo bayan cin amanar da kika yi min na hadani da 'yan tsibbu" Ga mamakin kowa durkusawa tayi a gaban Maamu zata dafata tayi saurin janye jikinta sai ga wasu zafafan hawaye suna ambaliya kamar famfo a idanun Gimbi "Maamu don Allah na tuba ki yafe min duk abubuwan da ake zargin nayi miki. Naji na karba amma ki yafe min. Indai don wannan ne aka sa ya auri Rumana ni ko me kike so daga yau na dauki alkawarin yi miki indai zai saketa" "Mutuwa ce kadai zata rabani da Rumana kisa wannan a ranki Gimbi" Awaisu ya bata amsa Tashi tayi tana share hawaye "wannan cin mutumcin da kayi min na rantse maka sai na rama. Yau ba don Rumana ka aura ba da ko kaki ko kaso sai ka sakeni. To amma abin kunya ne a gareni aurena ya mutu akan wannan yarinyar da bata gama zama mace ba. Banda son zuciya irin naka da na iyayenta ina zaka kai ta" Baaba Hure ce wannan karon ta daka mata tsawa wanda yasa ta fita daga falon ranta yana kuna. Dakin da ta sauka ta shiga ta harhada kayanta cikin sauri ta janyo akwatin tsakar gida. Budar bakinta ta soma kiran yaranta "Har....bari mu koma gida ko me zan yanka domin canja maka suna sai na canja don bazaka taba tashi da sunan makiyana ba" Daga falon suka ji tana kiran 'ya'yanta Awaisu ya taso da sauri. Tare suka taho da sa'aninsu na gidan saboda dama wasa sukeyi a can baya. "ku wuce ku dauko kayanku tafiya zamuyi." Ta fada fuskarta babu alamun wasa. Amir ne yace shi dai a nan zaiyi hutunsa. Ai kuwa Gimbi ta surfa masa na maguzawa zata huce haushi a kansa. Awaisu ta gani yace yaran su koma ciki. "Ni da 'ya'yana ta yaya kake so na barsu a gidan nan?" Ganin suna kallonsu da fargaba a idanunsu yasa Awaisu cewa "Haris ku tafi tafi ciki kunji. Mummy is very sick. Irin zazzabin da Mu'allim ya taba yi yana ta surutu ne ya kamata. Yanzu zamu je asibiti daga nan a mayar da ita Abuja. Mu kuma ranar sunday sai mu tafi tare ko " Da tausayin mahaifiyar tasu Haris da kannensa suka koma har suna yi mata sannu. Bude baki tayi zata fara masifa Awaisu yayi mata wani irin kallo duk rashin kunyarta sai ga bakin hangame a iska ta kasa furta koda kalma daya. Matsowa yayi kusa da ita harda daukan akwatin saboda yaransa da basuyi nisa ba sannan ya rage murya yadda zata ji "Kada kiyi yunkurin daga murya a gidan nan wallahi zan baki mamaki. Ki duba ciki da waje baki da mai kwatarki idan kika shigo hannuna domin kin gama bata rawarki da tsalle a idanunsu" Bata iya sake tanka masa ba ta bi bayansa har mota. Dreban ya kira gefe ya ja masa kunne sosai akan cewa kada ya kuskura ya tsaya ko ina sai Abuja. Sannan ya kara da cewa idan sun isa ya karbi mukullin motar Gimbi yace zai sha mata mai. Idan ta bayar ya hada da na motar da suka zo ya tafi kada ya dawo gidan sai ya neme shi da kansa. Dreba mamaki ya ishe shi amma baice komai ba. Dama ba dadewa yayi a gidan ba bai san meye tsakanin ma'auratan ba. Baya Awaisu ya zauna kusa da Gimbi ya zaro kudi ya damka mata. "Ga wannan ki rike ko bukata zata taso miki kafin na dawo. Sannan naji labarin za'a fara wahalar mai nace Gambo ya tafi da motarki ya sha miki mai idan kun isa. Sannan bana so kina tada hankalinki don kinsan bana jindadin ganinki a haka. Ki tafi kafin nasan yadda nayi na kawar da matsalolin dake son rabamu" Bacin ranta taji ya fara sauka kadan saboda a tunaninta ko akwai sauran asirin da yake aiki a kansa. Ba dai tace komai ba don burinta kawai ya fita daga motar ta kira Ovi. Sallama yayi mata harda sakin fuska ya koma cikin gidan. Yana fita ta kira Ovi ta juya harshe da turanci tana kuka tana fada mata me ya faru. Ovi dama a speaker tasa wayar ita da Rita sukayi dariya mai isarsu sannan tace zata jirata idan ta dawo su koma wurin Boka. Har tuna mata takeyi tasan dai aikinsa babu wasa kaifi daya ne. Gimbi taci kukanta dai kafin su isa. Kamar yadda aka umarci dreba ya karbe mukullin motarta da na wadda suka zo yayi tafiyarsa. ***** Da Awaisu ya koma ciki sun cigaba da tattaunawa inda 'yan uwansa mata suka nuna tsoron kada Gimbi ta koma wurin da take karbo kayan asirinta. Nan ya fada musu umarnin da ya bawa Gambo dreba da kuma kashedin da yayiwa maigadin gidansa a waya kan cewa kada ya bar kowa ya shiga ko fita daga gidansa har sai ya dawo. Baaba tace duk da haka sai ya tashi tsaye sosai da ibada saboda ta nan bangaren yayi raunin da aka sami galaba akansa duk da tasan cewa asiri gaskiya ne. Bayan nan suka ce ya kamata aje har gidansu Gimbi a fadawa iyayenta abubuwan da suka faru. Awaisu yace dama yayi niyar idan ya koma yaje "Ba'ayi haka ba. Wannan ba maganar mutum daya bace. Idan ka tashi tafiya sai mu tafi tare har da Harisu ko wani cikin kawunnai domin su dauki zancen da mahimmanci" inji Anti Baraka. Maamu da Baaba ne sukayi ta saka musu albarka sannan suka tashi domin yin sallar laasar. Kafin su fita Mama uwargidan Harisu tana dariya tace "akwai fa amaryar da bata san an aurar da ita ba.".. Tsokanar Awaisu suka fara har suna cewa ya tsaya su gaisa da surikinsa suna dariya. ita dai maman Rumana ficewa tayi. Ko ita bazata iya kishi da Gimbi ba bare Rumana. Auren nan don dai kawai anfi karfinta ne. Amma tana jin tsoron yadda zaa zauna gashi bai saki Gimbin ba kamar yadda yace zamansu tare ya rama abubuwan da tayi masa shine kawai zaisa ya huce. Kowa ya fita daga dakin ya rage Awaisu da Harisu. Wani nauyin yayan nasa yake yi. Harisu ya kula dashi ya dawo kujerar kusa da tasa "Menene yake faruwa Awaisu?" Iska ya dan furzar "Yaya don Allah hankakinka ya kwanta da auren nan? Wallahi bana son abin da zai zo ya taba zumuncinmu ko kadan" Zulumi da fargaba ya gani a cikin idanun kanin nasa. Da farko shima auren nan bai wani kwanta masa ba amma yanzu yaji dadin wannan hadin. "Awaisu abu daya kawai nake so ka fada min shine dalilinka na saurin amincewa da auren" Abin mamaki ga Harisu gani yayi kanin nasa ya dan dukar da kai kafin ya bashi amsa "Abin da ban taba tunani bane ko a mafarki Yaya shine jin soy....uhmmm...soyy" Shiru yayi ya dafe goshi ya dago kamar zaiyi kuka "kunyarka nake ji" Harisu ya kwashe da dariya irin wadda Awaisu ya dade bai ga yayi ba " kaima yadda akace shiru ko kunya a wurin budurwa amincewa ne to kaima kunyarka ta cire min duk wata damuwar da tayi min saura. Nasan Awaisu a matsayin kani kuma dan uwa nagari. Fatana ka zamewa Rumana abokin rayuwa nagari. Na sani ko babu ni iyalina bazasy taba tagayyara ba idan kana raye. To menene abin fargaba idan kana auren 'yata." Shi dai Awaisu godiya yayiwa yayan nasa sosai suka tafi masallaci. ***** Wurin biyar da rabi na yamma Rumana ta dawo daga gidan kitso. Ana mata fadan dadewa tace kawayenta na primary ta hadu dasu a gidan suka tsaya hira. Sai da taci abinci aka kirata dakin Maamu. Bata kawo komai ba ta tafi. Da shigarta ta fada jikin Maamun tana murnar ganin kara samun lafiyarta. Baaba tace to ta tashi dai kada ta karyata. Baaba tace "Rumana kin tuna duk wahalhalun da kuka sha da Maamu a Abuja ko" Tace eh yaushe zata manta. "A dalilin haka kawunki ya kara aure yau dinnan kuma muna fatan wannan karon in sha Allah an dace da matar kwarai" Baaba tana magana tana kallon yanayin fuskar Rumana. Murmushi tayi mai nuni da farinciki "dama jiya ya fada min zai kara aure ashe abin ya matso haka. Yeeyyy zamu sha biki...." tashi tayi zata fita tayiwa 'yan uwanta shela Baaba tace ta dawo ta zauna. A dofane take don sauri take ta samu ta fita ta kai musu labari. Dole suyi shagali wallahi ko don ta konawa Gimbi rai saboda bata san Gimbin ta tafi ba. "Nasan bazaki so Maamu ta sake zama irin na da ba a gidansa ita kadai da Gimbi.." Rumana ta firfito da idanu tana kallon Baaba kafin ta dafe kirji a dan tsorace "Ba dai Abujan kuke so na kara zuwa ba. Ni wallahi bazan koma ba" "Wane irin zance ne haka ina magana kina cewa bazaki koma ba?" Baaba ta fada cikin fada. Kafin ta kara cewa komai Rumana ta tashi tana bubbuga kafa ta fita daga dakin. Ko dukanta Baba zaiyi bazata yarda ta koma Abuja ba. Wa yasani ma ko matar tafi Gimbi iya mugunta. Maamu ta kalli Baaba tace "gashi nan kince na bari ki fada mata har ta fita baki fada ba sai kara hargitsa mana ita da kika yi" Rike baki Baaba tayi "to ni dai babu ruwana kuma iyayenta su karata. Wannan yarinya da gani zaayi daru da ita" ***** Tun da ta shiga daki take ta kumburi taki fita falo. Bayan isha kanwarta Hafiza ta sanar da ita babansu yana kiranta a dakinsa. Tashi tayi da kudurin ko me zaice zata dage bata koma Abuja ba. Mamanta ta gani a gefensa fuskarta babu wata walwala. Zama tayi ta gaishe shi. "Rumanan Baba kuna magana ashe dazu dasu Baaba baki gama ji ba kika tashi" Kuka ta soma yi masa. Dama plan din da tayi kenan tayi ta kuka tana rokonsa ya barta a nan. "Baba bana son sake zuwa Abujan ne" "Naji Rumana amma ai baki tsaya sunyi miki cikakken bayani ba. Dazu auren dake aka hada" Zama tayi dabas daga dan durkusun da tayi "Baba ni me nayi kuma zaka min aure? Shi wannan dan Baban bayan gidan Allah bana sonsa. Kuma ko makaranta ni ban gama ba" Kuka ne ya kwace mata ta tashi ta fita muryarta har ta soma karade gidan ta shige dakinsu ta kuka. Harisu ya kalli mamanta "ko sunan mijin ban fada ba kinga ta tashi" Da alamun rashin damuwa don ita fa auren nan baiyi mata ba ta tabe baki "ni meye nawa a ciki?" Kusa da ita ya koma ya rungumota "kinsan ina alfahari dake saboda saukin kai " "Shiyasa zaka cutar min da 'ya" ta amsa mai da hawaye "Kiyi hakuri. Nasan ko ba Gimbi yake aure ba dole abin nan yazo mana wani iri. Amma ki kyautata zato ga Allah in sha Allah auren nan alkhairi ne" Wayarsa ya dauka ya kira Awaisu ya fada masa yadda sukayi "Ka tura a kira maka ita kayi mata bayani da kanka" Awaisu ya kalli su Baaba da suka gama fada masa ya suka kare da Rumana dazu. Allah gani gareKa yace sannan ya fita ya ce a fada mata ta same shi a falon Harisu. Kukanta ne ya fara sanar masa da isowarta ta shiga ko sallama babu. Wuri ya nuna mata a kujerar kusa da wadda ya zauna. Ta zauna idanunta a kumbure ta sake fashe masa da wani kukan "Uncle aure akayi min" ta fada murya na rawa. Tausayi yaji ta bashi "kiyi hakuri, kinsan komai nisan lokaci dama wata rana zakiyi aure" Bakinta ta turo tana wani hawayen "to kuma ni sai ayi min auren dole ko karatu ban gama ba. Kuma ko sonsa banayi" Awaisu yayi murmushi "indai karatu ne zan barki kiyi ta yi har sai kin gaji don kanki" Dagowa tayi suka hada ido yaji wani sonta ya kara shigarsa. Ita kuwa murmushi ta danyi "Allah da gaske zaka yiwa ko waye mijin magana ya barni nayi karatu? Daga nan ma ka roke shi ya sakeni kawai." Ta dan cije lebe cikin takaici "nasan ba kowa bane mai nacin nan sai wannan dan abokin Baba da na fada maka" Dariya Awaisu yaso yi jin tace mai naci. "Bana fatan ki fito daga gidan mijinki indai ba da sunan zuwa unguwa ba. Ko kin yarda zaki bini Abujan?" Duka biyun babu wanda yayi mata. Amma idan ta tuna yadda ta tsani yaron nan mai naci sai taji gara Abujan "To amma don Allah uncle idan anje Abujan ka damka ni a wurin Anti Amarya" "Umm Ruman kenan, wato Anti Amarya ko don iya dadin baki" yayi dariya yana kallon yadda ta hade fuska ita da gaske take. Goge hawayenta tayi ta tashi "to yaya sunanta?" "Umm Ruman Harisu Sa'ad" Idanunsa ya kafeta dasu yana kallonta babu alamun wasa. Jikinta tuni ya fara wani irin rawa "Ni Rumanan?" Sai da ya tashi tsaye ya rungume hannuwansa a kirjinsa sannan ya gyada kai "ke Rumanan" Wai me yake fada ne. Kanta ta nuna da hannu tana masa kallon rashin fahimta "Uncle ni ka aura? Innalillahi" Kafin ya ankara tayi hanyar fita daga falon. Da saurinsa ya isa bakin kofar ya rufeta da kafarsa tare da riko Rumanan. Kuka ta fashe masa dashi tana kokarin kwacewa. Rungumeta yayi yadda bazata iya kwacewa ba tana kuka tana maganganun da baya fahimta sosai "Uncle bazan iya ba. Ka rufa min asiri. Wayyo Allahna. Kalli ka gani fa nice 'yar karama dani..." Hannu yasa akan bakinta yace "shhhh Umm Ruman everything will be okay I promise." Tun tana kokawa dashi na son kwacewa daga jikinsa har ta gaji ta dena. Ji yayi ta dena kokarin kwacewa sai ajiyar zuciya da take yi lokaci-lokaci. [15/08, 17:46] ‪+234 803 272 5896‬: *KASHE FITILA* 💡38 *Batul Mamman*💖 Tausayi Rumana ta bashi sosai sai dai kuma baya jin zai iya rabuwa da ita a yadda yake jin soyayyarta a ransa. Cikin 'yan kwanakin nan komai nata burge shi yake yi. Hannunta ya kama suka koma wurin kujera amma da kyar ya samu ta zauna kanta a kasa taki dagowa. "Dago ki kalleni" yace yana leken fuskarta. Maimakon ta dago sai ta cusa kanta a tsakanin cinyoyinta gabanta yana tsananta bugu. Abu ne kamar a mafarki wai Uncle Awaisu ya zama mijinta. Kyaleta yayi don baya son takura mata. "Ki dena kukan nan kada ki fita ido a kumbure. Just calm down idan kin sami natsuwa ki shiga ciki" Zumbur ta mike suka hada ido tayi saurin kawar da fuskarta. Idanunta banda kumburi sunyi ja sosai. Kafin ya sake mata magana ta fice da gudunta don ma kada ya sake tsareta. Komawa yayi ya zauna yasa hannu yana matsa gefen kansa da yake masa ciwo. Abubuwan da suka faru dashi a tsukin kwanakin nan sun daure mishi kai haka kuma dasu yake kwana yake tashi. Rumana na fita dakin Maamu ta tafi suna tare da Baaba. Tana shiga ta fada jikin Baaban ta fashe da wani irin kuka. Bayanta Baaba tayi ta shafawa tana rarrashinta. Maamu itama rarrashin take yi. Ta dauki lokaci a haka kafin ta dago kanta "Baaba don Allah kuce ya sakeni. Ta yaya zan auri Uncle don Allah" wani hawayen ke bin kumatunta ta rinka bin kakaninta da ido. "Kul Rumana kada na sake jin zancen saki a bakinki" cewar Baaba "Ni wallahi bana son aure yanzu. Yanzu sai ayi ta cewa na auri kanin Babana. Kuma ma ko sonsa banayi" "A'uzubillahi" Baaba ta fada tana doke bakin Rumana. Bare baki ta sake yi Maamu ta janyota jikinta. Maamu tace "Rumana ba kya sonsa? To babu maiyi miki dole " Dan kunya taji "ina sonsa mana Maamu amma ba son so ba" Dariya suka so yi su biyun sannan Maamu tace "to wanne kike masa.? Bansan meye son so ba" "Ina nufin ina son shi amma ba na soyayya ba" ta kare a hankali muryar ma bata fita sosai saboda yadda taji kunyar abin da take fada. Baaba ta rike haba, gaskiya akwai rigima don tayi zaton Rumana tafi haka wayo sai gashi ta gane har yanzu tana da sauran wauta. Wai son so, saura son ki. Rarrashinta suka rinka yi da ban baki don ranar a dakin ta kwana. Washegari ko alamun Awaisu bata gani ba ashe ya tafi gaishe da dangin Maman Rumana tunda basu san da auren ba shi kuma lahadi yake son komawa. Da kanin Malam Saad babansu Harisu da kuma kanin Maamu suka je sanar da kakan Rumana na wurin uwa domin fita hakkinsu tunda abin yazo babu shiri basu sani ba. 'Yan uwanta sunyi mamaki sosai amma sunsa albarka tunda an riga an daura sai fatan zaman lafiya. ***** Gimbi ta gama shirinta da sassafe ko ruwa bata iya sha ba ta fito tana neman keys din mota sai dai babu ko daya. Tunawa tayi ta bawa Gambo dreba ta fita ta tambayi maigadi ko ya bashi da ya dawo da motar don ta ganta a cikin gidan. Maigadi yace ai bai ma fita da ita ba tun a jiyan. Abin ya bata haushi ta kira wayarsa yafi a kirga amma yaki dauka. Matarsa har cewa tayi ya dauka mana matar oga ce yace umarnin ogan yake ba. Iyakar kulewa Gimbi tayi gashi tun a hanya take kiran Ovi da Rita bata samu. Data dawo gidan bata ga Rita ba duk ta damu. Shiyasa duk irin gajiyar da ta kwaso ko runtsawa bata sami yi ba saboda tunani. Tsaki taja ta nufi gate tana ta masifa. Isarta ke da wuya tace maigadin ya fita ya nema mata taxi ya dan sunkuyar da kai "Oga yace kada a bari ki fita har sai ya dawo" Kallon rainin hankali tayi masa sannan ta daka masa tsawa "Zaka bude min ko sai nasa an koreka a yau dinnan?" Matsawa yayi ya bata wuri taje taji kofar garkame da kwado. A fusace ta koma ciki tana ta kai kawo. Da ta gaji ta sake dawowa ya kuma tabbatar mata bazai bude ba. Suna haka tana ta sauke masa kwandon zagi suka ji bugu. Tambayar ko waye yayi Rita ta amsa. Gimbi har ta soma jindadi zai bude ta samu ta fita sai ta ga ya koma kan kujerarsa ya zauna. "Kai malam baka ji ana buga kofa ne?" "Oga cewa yayi babu shiga babu fita" ya amsa mata. Kallon mamaki tayi masa "ina jin baka ganeta ba. Rita ce mai aikina" "Hajiya kiyi hakuri ko ki kira shi a waya. Ni dai abin da ya fada min kenan" Jikinta har tsuma yake yi don bacin rai ta kira Awaisu. Lokacin tasowarsu kenan daga wurin kakan Rumana zasu tafi wurin da ya ajiye mota. Sai da ya bari ta kira sau biyar a jere sannan a na shidan ya dauka. "Ina jinki" ya fada muryarsa na nuni da baya maraba da wayar. "Abin da zaka ce min kenan bayan jiya ka yaudareni kasa na bada mukullin mota ko. Wallahi baka isa kaci mutumcina ba kaima ka sani" "Meye dalilin kiran naki yanzu I am busy?" "Sannu agogo sarkin aiki. Ba wani abu bane kasa maigadinka ya bude min kofa na fita " "Babu mai fita ko shigar min gida sai na dawo" Bacin ranta ne ya karu "to kace ya budewa Rita ta shigo" Dadi yaji ashe matar da baisan daga ina ta samota ba bata gidan. Murmushi yayi kafin yace "wani abu ne haka Rita din?" Wulakanci! Lallai Awaisu bai santa ba har yau. Danne bacin ranta tayi domin burinta ta fita da kanta taje wurin Boka. Daga shi har dangin nasa sai ta mayar dasu waina don juyasu zata rinka yi. "Awaisu kaga na shanye duk wani abin da 'yan uwanka suka yi min. Ka barni naje gidan iyayena mana..." Shiru taji na dan lokaci bai amsa ba sai kuma taji yayi yar siririyar dariyar da take matukar so a wurinshi. Kashe murya taji yayi yana magana kasa-kasa "ashe haka kike da rigima my little princess, don kina son tausa sai kin haye min cinya" Hannun da Gimbi ta rike wayar dashi ne taji ya fara karkarwa kafin duka jikinta ya dauka. Wayar da kanta ta subuce ta fadi a kasa ta tarwatse. Kunnenta ta kaiwa duka tana son tabbatar da abin da Awaisu yace....runtse idanu tayi tana hango Rumana akan cinyar Awaisu. Wani irin ihu ta saka na tsananin bacin rai "Awaisuuuu, karyarka ka hadani da wannan afiruwar. Rumana tayi min kadan sai dai nayi da uwarta. Dani kuke zancen duka, sai na baku mamaki." Da kyar ta iya jan kafarta ta koma cikin gidan bayan ta hada wayarta. Rita ta dannawa kira tana bata sako zuwa ga Ovi da bokansu Shirun da yaji daga bangarenta yasa shi kwashewa da dariya har idanunsa na kyalli. Mara kunyar karya ya fada yana komawa wurin motar ya shiga. Dama wadanda suka zo har sum shige ganin yana waya. Gidajensu ya kaisu tare da godiya da alkhairin da ya saba musu. ****** A daki Rumana ta wuni har dare taki cin abinci. Mamanta tayi fadan ta gaji ta fita harkarta amma duk ta damu. Gashi tun baaje koina ba ta wani fige ina ga ta fara zama da Gimbi. Da daddare Awaisu da Harisu shawarwari suka yi da iyayensu mata akan yadda zasu gabatar da komai na lamarin Gimbi. Da sassafe zasu tafi Abuja tare da Harisu da Anti Baraka. Yaso ganin Rumana amma baya son zakewa duba da rashin walwalarta tun bayan ta sami labarin shine mijin. Ajiye komai zaiyi yanzu sai ya koma Abuja yayi 'yan shirye shirye da bincike akan Gimbi. Ranar lahadi karfe takwas na safe sun gama shiri yaransa suma sunyi wanka sunci abinci ana ta fitar da kaya mota. Awaisu yana son ganin Rumana amma yayi wuri. Dakin Baaba yaje yi mata sallama yayi sa'a Rumana tana kwance akan gado ta kudundune jiki da bargo. Yasan me yiwuwa Baaba na tare da Maamu ya danyi murmushi sannan ya karasa bakin gadon ya zauna. Yana zama yaji alamun Rumana ta dan matsa baya yayi murmushi wato taji shigowarsa. Ashe tun kafin ya shigo idonta biyu baccin karya tayi saboda shi. Kamshin turarensa ya mamaye dakin a hankali ya bude bargon saitin fuskarta da take kallon bango ta juya masa baya. A saitin kunnenta har tana jin numfashinsa taji ya soma magana a hankali "Ki kular min da kanki sai nan da wata daya zan dawo in sha Allah. Idan kina bukatar wani abu kada ki tambayi kowa ki kirani" A takure take sosai ga wani sabon yanayi Uncle ya wani zauna kusa da ita haka. Hannunta ya lalubo ya dora mata waya mai kyau. "Akwai kudi a ciki kuma na saka miki numbers dina. Zan jira wayarki ta tambayata yaya hanya." Ji tayi kamar ya sake kwantowa jikinta ta kuwa runtse ido tam. Wani murmushi yayi ganin yadda tayi masa kyau. Ya cigaba da magana "a hankali zan koya miki yi min son so kamar yadda nake yi miki idan kin dawo Abuja" Bata san lokacin da ta bude ido ba tana mamaki ko su Baaba ne suka fada masa. Kamar ya karanci me take tunani yace "Indai bazaki rinka yi min magana ba to duk wanda kika yi hira dashi zan roka ya fada min tunda kina min rowar muryarki. Na tafi" Wani gwauron numfashi ta saki da ya tashi. Sake juyowa yayi "Babu yiwa miji addua? Kina wasa da ladanki da kin magana Princess" Bargon taja ta rufa har kanta sannan kamar bazata yi magana ba yaji tace "Allah Ya kiyaye" Fita yayi yana murmushi shi kadai yana cewa "soon Umm Rumana, very soon zan koya miki karatun da ni kadai ya dace na koyar dake." Ita dai bata fito ba har taji ana ta sallama dasu sannan taji alamun duka an watse daga tsakar gidan. Tashi tayi jiki babu kwari don babu wani abin kirki a cikinta ta daga wayar tana kallo. Waya ce mai kyau ta zamani. Murna ta fara sai da ta tuna batun auren ta cusata a kasan pillow ta koma ta kwanta. Wurin karfe uku Mamanta ta leko kiranta. Har yanzu Baaba bata dakin gata ko wanka bata yi ba ita tana fushi anyi mata auren dole. Dakin Maman taje tana shiga ta ga Umma yayar Mama dake aure a Lagos. Da yake sun dade rabon da su hadu saboda zamanta a Abuja a kunyace ta gaisheta. Umma ta dagota tace "yata kamar ba amarya ba duk kin rame" "Babu abin da take ci sai kuka Yaya" inji Mama Umma ta bata fuska "wai haka Rumana?" Bata jira amsarta ba ta dauki plate daga kayan abincin da Mama tasa aka kawo mata ta zuba abinci sosai a kai ta saka cokali biyu tace suci tare. Rumana zata fara gardama Mama ta soma mata fada. Umma tace ta tashi ta barta da 'yarta. Ba musu ta fita ranta duk a bace. Bayan ta fita ya rage su biyu kawai. Da nasiha Umma ta samu suna ci tare tana fakewa da hira Rumana ta cinye fiye da rabinsa Umma na tsakura. Dama wayo taso yi mata. Suna gamawa tasa taje tayi wanka ta shirya sannan tayi sallar laasar. Can yamma Umma tasa Hafiza ta dama mata kunu ta shanye sannan da daddare suka ci tuwo tare. Sai da suka gama Umma ta kirata cikin uwar dakin mama tace ta zauna magana zasuyi. "Rumana kinga da yanayin da aure yazo miki ko" An tabo inda keyi mata kaikayi ta soma sharar kwalla "Ba kuka nace kiyi ba. Rumana ki daga hannu ki godewa Allah. Ko kinsan mata nawa ne da kyau da ilimi da komai na tarbiya Allah bai basu mazan aure ba? Duk hukuncin Allah ga bawa alkhairi ne sai dai idan bawan ya bijire " Shiru tayi tana sauraron Umman. "Rumana naji labarin komai a wurin Binta kuma na tausaya miki Allah Yasa anyi bayan nazo gari. Sai dai ki sani damuwar nan da kike yi ita tasa mamanki ta kasa kwantar da hankalinta. Wanda hakan ya janyo ta kasa hakura yadda babanki yake ta bata shawara. Shin kina son zama sanadiyar kawo sabani cikin rayuwar iyayenki?" Da sauri ta girgiza kai. Umma tace "ki koyi hakuri tunda girma ya hau kanki. Aure daraja ce da rufin asiri ga maauratan" A hankali tace "ko da mijin babba ne Umma" "Da babba da yaro basu da bambanci matukar sun iya kula da tattalin iyalinsu. Ina so ki nutsu ki sani cewa yanzu ke ba karamar yarinya bace saboda haka ki ajiye duk wata wauta da shirme a gefe. Gimbi da zaki zauna da ita idan kika tafi a haka zaki kwashi kashinki a hannu" Rumana me zatayi in ba dariya ba da jin wannan maganar. Umma taji dadin ganin ta sake ta hau bata shawara da kwantar mata da hankali. Daga karshe tace "Binta tace wai sai kin gama secondary nan da kusan wata biyar zaki tare amma mijinki yace a can Abujan yake so ki karasa. To nidai nasan a da ne ake irin wannan auren har ma a shekara amarya lafiya kalau. Yanzu kuwa indai ba so suke a kaiki da ciki ba gara ayi abin da ya sauwaka ki tare kawai" Gaban Rumana ya fadi ta hau zare idanu. Ita ta manta ma ana tarewa idan anyi aure. Shikenan sai su zauna da Uncle Awaisu......ita kam bazata iya ba. Umma ta katse mata tunani "Rumana ki sani Allah baYa dorawa bawa abin da yafi karfinsa. Saboda haka ki kwantar da hankalinki ki fuskanci sabuwar rayuwarki. inaso ki kiyaye idan an kaiki ko ruwa kada Gimbi ta baki kisha, addua kuma kada ki kuskura kiyi wasa da ita. Sannan ki sani cewa kina da babban makamin jan hankalin miji wato kyautatawa mahaifiyarsa. Ina mai tabbatar miki tunda Gimbi ta wulakanta masa uwa yanzu ko pure water kika bata wallahi sai kin kara shiga ransa. Ina fada miki don kada ki sakankance wai baya sonta ko abu makamancin haka. Tsakanin mata da miji sai Allah. Sai kiga mace da mugun hali ko kazanta miji yana korafi amma ya saka rabuwa da ita saboda aure rai gareshi" Maganganun suna ta shigar Rumana har inda Umma tace ta cire zancen saki a ranta ta karbi kaddararta hannu biyu. Idan tayi haka da zuciya daya to lallai zaa wayi gari ta kamu da son mijinta. Abin da kamar wuya take ji amma yadda Umman lagos take ta rarrashinta da bata baki yasa taji zata yi kokari ta daure ta zauna dashi. Amma fa a ajiye maganar aure a gefe ita kam bata girma ba gaskiya nauyinsa take ji. ***** Su Awaisu sun isa ido na ganin ido. Yara suna ta murnar ganin Gimbi amma taki kulasu ko fitowa daga dakin ta kasa. Sai da suka fada mata da su wa suka zo ta fito babu shiri. A falo suka hadu Awaisu yana cewa Anti Baraka ta shiga daya daga cikin dakin baki zai kawo musu abinci su ci. Gimbi karasa fitowa tayi ta rinka jan tsaki tana harararsu. Babu wanda ya kulata sai Haris da yake kallon yadda take yiwa yayyen babansa yana jin babu dadi. Ganin Awaisu yayi hanyar dakinsa suma kowa ya tafi masaukinsa ta bishi dakin sai dai tana zuwa taji ya rufe da key. Wanka yayi ya fito ba dadewa Gambo ya kawo abinci mai rai da lafiya da Awaisu yace ya siyo musu sannan ya bashi mukullan motocin. Duk yadda taso yi masa magana yaki. Gashi bata son basu fuskar ganin yana mata wulakanci. Shi da yaransa dasu Harisu suka ci abincin suka koshi sannan kowa yaje ya kwanta. Washegari kafin shabiyun rana sun fita Gimbi tana ta tunanin uban me ya kawosu gidan. Gidansu Gimbi suka je sunyi sa'a iyayenta duka suna gida. Bayan gaishe gaishe Alh Mudi bai boye musu mamakinsa na ganinsu ba saboda baiyi zato ba. Anti Baraka ita ce tayi musu bayanin dalilin zuwan nasu. Domin shaida harda hoton Maamu a asibiti ta nuna musu. Mama tana gani sai kuka. Idan kaga Maamu a lokacin da cuya kace zata yi rai ma. Shi kanshi Alh Mudi idanunsa ja sukayi yana mai bakincikin Gimbi tsatsonsa ce. "Alh Harisu wallahi na baku wuka da nama duk abin da kuka ga ya dace kuyi mata domin huce wanan bakincikin kuyi. A matsayina na mahaifinta kuma nayi alkawarin zamuje fika dubo maamu kuma mu basu hakurin bata musu zuria." Mama kuka ne kawai yaci karfinta ta shige daki ta barsu. Allah Ya isa Bebi. Alh Mudi ya jajanta musu sosai karshe dai sun tsayar da magana akan Awaisu zasu je har gidan su yiwa Gimbi fada. Mamakin dalilinsa na kin sakinta ma sukayi. A ransa yace idan har ya saketa wallahi taci bulus karawa gaba zatayi wani mai rabon wahalar ya dauka. Washegari da safe su Harisu suka kama hanya suka koma. Duk bakin nacin Gimbi fita ta gagara. Ga kudi ta turawa Ovi masu yawa sunce an karbo magunguna amma babu damar kawowa gidan. Gimbi tayi haukan tayi borin duk a banza. Shi tsoro ma yake kada ta bata masa yara. ***** Yau kwanansu Awaisu biyar da komawa Abuja Rumana tana cin kosai bayan tayi buda baki na azumin nafila da takeyi ranar litinin da alhamis taji wayarta tana ringing. Tun da ya bata wayar bata bawa kowa number ba kuma bata kira ba. Ajiyarta take yi kawai. Uncle taga an rubuta tayi saurin yin baya kamar shine da kansa. Mama tana kula da yadda tayi ta dan sha kunu tace ta shiga daki ta dauka mana. Gabanta yana faduwa ta dauka ta kara a kunnenta a dan tsorace. "Assalam alaikum" Wani sanyi yaji ya ratsa masa zuciya ya danyi murmushi a ransa yana mamakin yadda yake jin Rumana. "Princess baki nemana ko? Har yanzu baki fara yi min son so din bane" "Ina wuni" ta gaishe shi zuciyarta tana ta bugu. "Ba amsawa zanyi ba tunda baki nemeni da kanki ba. Dama kira nayi naji ko kina da bukatar wani abu" Murya can kasa tace "babu komai" "I miss you" Wani irin faduwar gaba taji shima kuma sai da yaji kunyar abin da ya fada mata. Amma sai ya sami kansa da son jin amsarta "Baki ji me nace ba?" Tunawa tayi Umman Lagos tace mata ta karbi kaddararta kuma tayiwa Awaisu biyayya. Budar bakinta sai cewa tayi. "Uncle I miss you too" kit ta kashe wayar ta dafe kirji tare da kurma ihu. Ita wallahi kwatantawa taso yi a zuciyarta taji ko nan gaba zata iya fada. Mama ce ta shigo dakin da sauri tace me ya sameta. Rumana dafe da kirji tace "Babu komai" Tsaki Maman tayi ta fita daga dakin. Awaisu kallon wayar ya rinka yi cike da mamaki kafin ya tashi ya bude wardrobe dinsa. Fika zaije gobe tunda zai kama asabar ya dawo lahadi kawai don ya ga Rumana [15/08, 17:46] ‪+234 803 272 5896‬: *KASHE FITILA*💡39 *Batul Mamman*💖 Bayan Awaisu ya gama hada kayansa sai kuma ya fara tunanin me zai cewa su Harisu idan yaje. Kullum suna waya, karewa ma Harisu ne mutum na karshe da ya kira kafin ya kira Rumana. Kuma bai ce masa zai je ba. Dan tsaki yayi tare da jifa da jakar yana murmushi. Wai shine yau yake kunyar Harisu mutumin da kafin Gimbi ta fara gwara masa kai baya boye masa komai. Da 'yar wani ya aura har shawara zai nema wurinsa akan yadda zai shawo kanta, amma yanzu babu hali. Can kamar an mintsine shi ya tashi da saurinsa ya dauko waya yana dariyar samun mafita. Anti Ummukulsum ya kira. Duk gidan idan aka cire Harisu to bashi da ta biyunta cikin 'yan uwansa. Tana daki 'autarta cikin mata wadda ta kasance tsiransu da Rumana babu yawa don bai kai shekara ta bawa Rumanan ba ta kawo mata wayarta da ta bari a kitchen. Ganin sunan Awaisu ta dauka ta soma tsokanarsa. "Ango kasha kamshi" Dariya yayi suka gaisa cikin barkwanci. Dan shiru yayi kamar tana wurin ya dan sosa kai "Yayata ta kaina alfarma fa nake nema" "Dama wannan waya cikin dare ai nasan ba a banza ba. Me kake so?" "Ina son tahowa ne gobe..." dan dakatawa yayi domin jin me zata ce. Anti Ummukulsum ta nunawa Iman kofa alamun ta fita. "Awaisu kada ka sami matsala a wurin aikinka fa. Yaushe ka koma har zaka dawo." "Kwana daya zanyi. Ranar lahadi da wuri zan tafi in sha Allah" Dan tsoro taji "ko dai wani abu ya faru?" "Ko daya. Zancen gaskiya amaryata nake son gani" Dariya sosai ta rinka yi masa tana tsokanarsa wai ya zama sabon shiga. Shi dai bai kula ba ya roketa akan ta san yadda zatayi Rumana ta wuni a gidanta gobe yadda idan ya iso zai taho nan su hadu saboda yana kunyar Harisu. "Kinga daga tafiyata a ji na dawo bansan yadda zan hada ido dashi ba. Kuma gaskiya ina son ta saba dani a matsayin miji kafin ta tare" Anti Ummukulsum tace "Da gaskiyarka amma tarewar nan fa naji ana shawarar ko nan da sati hudun da kace zaka tafi da ita tayi karatu zata tare kawai." Murmushi yayi saboda ko kadan bai so ba da matan Harisu suka dage wai sai ta gama makaranta zasuyi biki. Shi ko me suke bukata zai basu idan ta taho karasa makaranta ta tafi kenan ita da Fika sai ziyara. Yaji dadi yadda yayar tasa ta bashi hadin kai zata aika Rumana tazo da wuri. Shima cewa yayi yana asuba zai taso "Amma me yasa baka taho yau ba bayan kun taso aiki?" Ta tambayeshi " 'Yar taki akwai mulki. Sai yau tayi min kiran da dolena nazo" ya kare yana dariya. Ji yayi Anti Ummukulsum ta dan dake murya "Ba kayi min dadin baki zan dauko maka matarka ba, wallahi kada kasa naji kunya nan gaba, ka dai san me nake nufi..." Dariya yake yi sosai harda rike ciki. Sannan yayi mata alkawarin bazaiyiwa Rumana komai ba. Tace gara dai ko meye idan tazo gidansa su karata amma ba da ita ba. Cikin nishadi sukayi sallama ya dan kashingida akan gadon yana danna waya daidai sunan Rumana kamar ji yake kamar ya sake kira. Gimbi ce ta turo kofar fuskar nan a hade tazo ta tsaya masa a ka. Ko dagowa baiyi ba bare ya nuna mata cewa ya ganta. Hannu tasa ta daki gefen gadon. "Malam ina da magana" Har lokacin bai dago ba ta fizge wayarsa tayi jifa da ita can karshen gadon. A daidai lokacin Abba yana yiwa Rumana downloading applications na karatu a wayarta yaga kiran. Sai da ya daga sannan ya mika mata ya tashi yace idan ta gama ta kai masa daki ya karasa. Hannunta har rawa ya rinka yi ganin sunan wanda ya kira. Ita da take jin kunyarsa me zaisa ya kuma kira. Haushi Abba ya bata don da ita ce da kyar idan zata daga wayar. A hankali kamar tana tsoron zai kamata ta dan kara wayar a kunnenta. Muryar Gimbi da taji yasa tayi kokarin kawar da wayar da sauri sai kuma ta fuskanci ba da ita take maganar ba. Yadda tayi masa jifa da waya haka ya tashi ya janyo hannunta ya wurgata kan gado yana daga tsaye ya dora kafarsa daya a kan gadon tare da dan rankwafowa. "Koda wasa Gimbi kada ki kara taba min waya bare har kiyi min jifa da ita" Wata muguwar harara ta sakar masa don bata tsoron ko me zaiyi mata. "Woooooo ka dai ji kunya ka rasa wadda zaka aura sai 'yar cikinka. Iyayenta kwadayi kai kuma son zuciya. Don kana waya da shegiyar yarinyar nan zaka tsareni da ido kace kada na sake taba maka waya. Idan na taba ka kasheni sai nasan cewa kaji haushi" "Kin gama?" Ya tambayeta yana kara matsowa kusa da ita. "Gamawata shine ka barni na fita daga wannan kurkukun saboda auroni kayi ba zaman prison nazo ba" Tana rufe baki yasa hannu ya kamo labbanta a tsakanin babban yatsansa da manuni ya matse iyakar matsa. Kokarin cire hannunsa tayi saboda azaba har tsakar kanta shi kuwa ya damke hannuwan da hannunsa dayan. Fuskarsa ce ta birkice babu alamun wasa ko kadan. "Ina so wannan ya zama karo na farko kuma na karshe da zaki zagar min mata. Idan baki sani ba to ina mai sanar dake wallahil azim a cikin abin da bai kai sati biyu ba Rumana ta shiga raina ina yi mata son da bana fata wata mace ta sake samun gurbi a zuciyata irin yadda ta samu. Aurenki Gimbi *kashe fitilar* rayuwata ne ya sanyani cikin duhu. Aurenta kuwa tun a yanzu nasan daidai yake da *kunna fitila* na ga haske a rayuwar da kika mayar bakikkirin" Yana magana yana murje mata labbanta radadi na shiga ga zafin maganganunsa gareta. Idonta ya cicciko zata yi kuka ya girgiza kansa. "Kada ma ki fara yi min kuka don baki ga komai ba. Ina fatan ko daidai da rabin son da nake yiwa Princess dina na samu daga gareta. A lokacin ne zakiyi kuka Gimbi. Nayi miki alkawari sai na baki mamaki kamar yadda kika sa kafa kika take soyayyata gareki kika nemi hallaka min mahaifiya." Sakar mata bakin yayi da yake tana da hasken fata bakin nan yayi jawur tasa hannu tana shafawa tana hawaye. Awaisu tayar da ita yayi yace ta fitar masa daga daki. Wani irin kallo take yi masa mai wuyar fassara. Yayi kama da kallon idan na sami dama sai na rama.... Sai da ya bari ta kusa kofa yace "nayi mantuwa" Gimbi ta juyo idanun nan sun kada sosai. Awaisu kwanciya yayi a kan gadon ko kallonta baya yi yace "wai dama ma'anar shegiya da kika kira min mata zan fada miki. Kinga wannan kalmar a tawa fahimtar ba ta 'yar da aka haifa a titi bace . Kalma ce ta matan da basa ganin darajar iyayensu balle suji maganarsu. Irin matan nan da suka fahimci aure a matsayin juya miji da ganin bayan suruka. Irin wannan matar Gimbi itace ta dace da kalmar. Saboda haka the next time da kika ji kina neman wadda zaki zaga da wannan kalmar to ki nemi mudubi ki kalla. Duk fuskar da kika gani itace she.... " Wayarsa ya hango tana haske kuma lokaci yana tafiya. Alama dai ta cewa ko dai an kira shi ya daga ko kuma shi ya kira. Bai karasa fadin abin da yayi niyya ga Gimbi ba ya daga wayar ya saka a kunne yana adduar Allah Yasa bata ji me suke cewa ba. Tun da Rumana ta dauki wayar ta soma kuka da taji maganganun da Gimbi ta yaba mata da iyayenta. Duk da taji sanyi a ranta saboda Uncle ya wanke Gimbi sosai amma a tsorace take. Me zai kaita gidan wannan mata a matsayin kishiya??? "Rumana kada ki kashe min waya magana zamuyi." Yasan indai bai hanata ba tabbas kashe wayar zatayi don ta gigita da taji muryarsa kuma yana jin sautin kukanta. Ajiyar zuciya kawai take saukewa saukinta ma ita kadai ce a wurin. Gimbi kuwa buga kofar tayi iya karfinta ta fita domin cigaba da tsayuwarta a dakin zai sa zuciyarta ta buga. Kwantar da murya yayi sosai ya fuskanci wayarsa ya manta da wata Gimbi "Banda abubuwan da suka faru dake da Maamu kinga irin rayuwar da Uncle dinki yake yi a gidansa. Umm Ruman don Allah kiyi min son so ko yaya ne domin na samu sauki a rayuwata." Rasa abin fada tayi ta share ido kawai tana jinsa. Abu daya ke yi mata yawo a zuciya shine ta bar jin tsoron Gimbi. Zata yi kokarin danne zuciyarta ta dena nuna tsoro a gabanta ko don ta tsira a gidan. "Yanzu haka zamu zauna dake kullum babu magana. Kuma bayan nasan kinyi missing dina" yayi maganar a sigar wasa. Da sauri kamar wani zai rigata tace "wallahi banyi ba dazu ma subutar baki ce" Tamkar yaro zaiyi shagwaba taji yace "Ayya Umm Ruman maganar nan kamar saukar tafasasshen ruwan zafi a tsakiyar watan March haka najita" Yana ji Rumana ta soma dariya harda kyakyatawa. Dama haka take ba wuya tayi murmushi ko dariya. Rayuwar gidansa ce ta canjata daga yarinya mai kazar kazar da yawan fara'a zuwa shiru shiru. Shima dariyar yayi sannan yace "Ina yi miki son so Rumana, don Allah kada ki bari na dade ina jira kema ki yi min irinsa. Nayi miki alkawarin baki dukkan kulawa kinji Princess dina" Maganganunsa sunyi mata nauyi dadinta daya ma a waya ne kila da ta tashi babu shiri. Shima Awaisu da yasan ya soma janyo hankalinta kyaleta yayi yace taje ta kwanta amma kafin nan ta yawaita addua. ***** Karfe goma na safe Anti Ummukulsum ta kira Maman Rumana tace don Allah ta turo mata ita tana nemanta. Mama tasan neman baya wuce nasiha game da aurenta tace zata taho nan da azahar. Anti Ummukulsum tace a'a yanzu take bukata don Allah saboda tana da uzuri a gabanta. Haka tayi ya 'yan dabaru dai Mama ta turo Rumana harda kaya set biyu wai kwana zata yi. Kafin shabiyu ta isa gidan Anti Ummukulsum tasa Iman rakata gidan kunshi nan kusa dasu. Bayan sun dawo Iman tayi mata kitso shiku kananu duk bisa umarnin Antin. Rumana dai bata san dalili ba tunda anyi mata lallen bati shikenan. Kafin tayi alwalar laasar Anti Ummukulsum din ta sake cewa tayi wanka. Iman ta kalla tana son tambayarta ko tasan dalili ita kuwa sai dariya take kasa-kasa. ***** Biyu da rabi a Fika tayiwa Awaisu. Yaran Harisu na ganinsa sai murna. Ihunsu ya sanarwa su Baaba zuwansa. Da ya shiga ciki Harisu baya gida yaje dakin Maamu ya gaisheta. Kamar ba ita ba ta kara cikowa ta murmure. Abinci ne mai rai da lafiya da fruits ake bata kullum banda su madara, nama da kwai. Duka sunji dadin ganinsa. Bai jima ba ya tashi ya tafi dakin da yake sauka. Mama uwargidan Harisu ke da girki har tana mita bai fada musu zai zo ba da tasa an gyara dakin. Wanka yayi ya kimtsa cikin kyakkyawar shiga ga kamshin da baya rabuwa dashi yana tashi. Da hularsa a hannu ya shiga daki wurinsu Maamu yace zai fita. "Daga zuwa kamar ana korarka zaka fita" inji Maamu. Dan sunkuyar da kai yayi "gobe zan tafi ne shiyasa nake son gama komai a yau" Baaba tace "har menene ya taso ka duk nisan tafiyar nan a yau kuma ka juya gobe?" Anti Amarya tana dakin ta tuntsire da dariya ganin yadda kunya ta hana shi sukuni. Babu wanda yasan Awaisu da kunya irin wannan sai fa yanzu da ya auri Rumana. Tana ta dariya tace "Don Allah ku barshi ya tafi. Yazo bai ga amaryarsa ba yaushe zai zauna" Maamu ta hau tafa hannu "da gaskiyar Haj. Umma da tace gara ayi bikin da wuri.. Baaba kinga ikon Allah yaran zamani" Baaba dadi taji har ranta Awaisu ya nuna da gaske yake son Rumana tace "tashi ka tafi kaji. Tana gidan Ummukulsum duk da dai yanzu zuciyata ta bani hadawa kuka yi kai da 'yar uwarka aka ce Rumana taje can" Godiya yayiwa Baaba wai ta taimake shi da ta sallame shi da wuri. Maamu ta jefeshi da lemon hannunta tana cewa babu mai kai Rumana gidansa sai ta gama makaranta. Shi dai fita yayi yana dariyar rigimar da yaji sun fara ita da Baaba akan tarewar Rumanan. Yazo fita Maman Rumana kuma zata shigo gidan. Rasa me zasuyi duk su biyun sukayi. Da can barkwanci ke tsakaninsu yanzu kuma matsayi ya canja. Da hular tasa a hannu dai ya durkusa harda sunkuyar da kai "Mama ina wuni" Ai kuwa Mama ta rikice tana cewa ya tashi shi kuma yana cewa sai ta amsa yanzu ita babarsa ce. Karshe dai ya tashi suna dariya yace "Daga yau irin gaisuwar da zan rinka yi muku kenan don gaskiya kunyarku nakeji" "Ka rufa min asiri don Allah kada ayi mana dariya" "Nagode da kika amince da auren nan. In sha Allah zan rike miki Rumana amana" Dan hawaye ne ya taho mata "dama can amanarka ce. Allah Ya baku zaman lafiya. Amma idan ka kara durkusa min kararka zan kai" Daga nan ta shige tana godiya ga Allah da Ya bawa 'yarta miji kamar Awaisu. Fatanta su zauna lafiya. A nasa bangaren sai yanzu ya sami kwanciyar hankali saboda baya so ko kadan ya zauna da Rumana wani cikin iyayenta baya so. Mota ya shiga ya sanar da Harisu isowarsa amma yanzu zai fita. Harisu shima yaji dadi domin ya fahimci zuwan na waye yace sai ya dawo zasuyi magana. Abinci da kayan sha Iman da Rumana suka kai falon mijin Anti Ummukulsum suka jere. Zasu fita ta dan ja hijabin Iman. "Yaya babba wai don Allah me yake faruwa ne? Naji kunce Abbanku yana Kaduna waye zai zo? Ko bako zakiyi?" Iman tace "hajiyar dadin baki ni dai bazan fada miki komai ba idonki zai gane miki." Gabanta ne ya fadi suna fitowa tana hada ido dashi. Idanunsa a kanta ta fara rawar jiki kamar wadda tayiwa sarki karya. Dauke kansa yayi suka gama gaisawa da Anti Ummukulsum sannan ta ce da Rumana ta shiga dashi falon ta zuba masa abinci. Hannun Iman tayi yunkurin kamawa ita kuwa ta zille ta matsa gaba ta gaishe shi ta shige ciki. Idanu kamar zatayi hawaye ta kalli Anti Ummukulsum sai ta ga tana girgiza mata kai ta dan sha kunu kada ma ta soma kuka. Tana kallo itama ta shige ciki aka barta da Uncle Awaisu a wurin. Gani yayi ta kasa motsi ya tako gabanta yazo ya kama hannunta ya shiga falon da ita. Bata san yadda zata kwatanta me taji ba da ya rike mata hannun. Shi kuma bai saketa ba sai da ya je gaban kujera ya dafa kafadunta ya zaunar da ita. Kasa kallonsa tayi ga kunya ga mamakin ganinsa a Fika a lokacin da bata yi tsammani ba. Gabadaya tayi masa kyau. Fuskarta dauke da kwalliya daidai misali ta saka riga da skirt sai karamin mayafi da ta yafa maimakon dankwalin kayan. "Wai me zanyi ki rinka yi min magana ne? Baki san musamman na taho wurinki kawai don kice min *I miss you* ba. Ko mun girmi wannan sai dai a fadi na gaban" ya kashe mata ido yana dariya. Hannuwanta tasa ta rufe fuska tana girgiza kanta "ni dai Uncle kunyarka nake ji" Zama yayi a kujerar dake kallonta ya duku kadan "nima fa kunyarki nake ji Princess. Yanzu sai muyi tunanin maganin kunyar tunda dai da bama ji ko" "Eh" ta ce a hankali. "To ki fara da yimin sannu da zuwa. Ance yana rage kunyar mata da miji" Murmushi tayi masa wanda ya kara mata kyau ta turo baki "Uncle nifa ba 'yar yarinya bace zaka yi min wayo" Tasowa yayi daga kujerar da yake ya zauna kusa da ita. Ta ganin haka ta matsa shima ya matso. Sake matsawa tayi taga ya kuma matsarta. A karo na uku ta kai jikin hannun kujerar shima ya matso ya zama babu wurin gudu. Mikewa tayi ya janyota tare da sakale hannuwansa ya zagaye kafadunta. A kunnenta yace "Ina zaki gudu kuma ke da zaki nuna min girmanki" Ji take kamar ta shige kasa ta rufe idanunta "Wasa nake yi Uncle yarinya ce ni ....sannu da zuwa. Yaya hanya? Ya su Amir?" Kansa ya dora a kafadarta yana murmushi cike da nishadi "Ni ban yarda ba gaskiya kin girma. Matan da suka girma kinsan da yadda suke tarbar mazansu ma kuwa?" Haushin kanta taji me ya kaita cewa ita babba ce. Gashi yana mata maganar manya duk kunya ta hanata sakat. "Ki juyo na fada miki yadda manya matan suke yi" ya fada yana kokarin juyo da fuskarta. Maganar wata malamarsu a Abuja 'yar Kano ta tuna a rude tayi saurin cewa "Wallahi da gaske ban girma ba. Malamar mu ta Civic education tace mu duka 'yan ajin kwailaye ne kuma wai kwailaye yarane" Duk da ta iya Hausa amma akwai kalmomin da suke kasancewa baki gareta irin wadannan. Dariya sosai Awaisu yayi har lokacin kuma bai saketa ba. Fuskarta ya rike da tafin hannuwansa ya matso da ita kusa da tashi. "Allah Ya faranta miki yadda kika faranta min. Ke kyauta ce gareni daga Allah. Allah Ya bani ikon rikeki amana kinji. Yayi min gata da yawa Ya kara min da Umm Ruman" Kokarin sauke kanta kasa take yi ya hana "Kada ki hada rowar magana da rowar ganin fuskarki. Wannan malama gaskiya idan mun koma ya kamata kije ki fada mata mijinki yace ke ba kwaila bace" " Da gaske Uncle?" Daidai kunnenta ya matsa ya fada mata wace ce kwaila Ihu ne kawai Rumana bata yi ba saboda tsabar kunya tamkar ta shige cikim kujerar. Shi kuwa Uncle Awaisu yadda take yi ne ya kara sanya masa nishadi a zuciyarsa ya kallon shirmen yarintar Rumana yana dariya.*KASHE FITILA*💡40 *Batul Mamman*💖 Hanyar fita ta soma nema yace ta dawo ta zuba masa abinci. Haka nan ta dawo ba don taso ba ta zuba ta mika masa plate din. Hanata tafiya yayi yasa ta zauna jingine da kujera da plate din a cinyarta shi kuma ya zauna daga gabanta yana ci. Duk lokacin da ta dago kai sai sun hada ido sai yayi murmushi. "Kin iya girki?" Tambayar tazo mata a bazata. "Uhm" kawai tace "Duk abinki sai kinyi min magana yau....kwaila kawai" Mayafinta taja ta rufe fuskarta a kunyace "haba don Allah Uncle" Yayi dariya "indai ba ita bace lissafa min abubuwan da kika iya dafawa" Dan kallon sama tayi kamar tana lissafi "tuwo, shinkafa, taliya, indomie, macaroni, suyar kwai da abubuwa da yawa" "Idan na sake dawowa abincinki nake so naci." Nan fa ake yinta. Girki yanzu take kokarin sake kwarewa. A da can tana koya a gida don har tana yi ma. Zuwanta Abuja da aka shata mata layi da kitchen yasa bata wani girki. Wanda ta iya dinma duk ta dan manta su. Dawowarta Fika ne Mamanta kamar tasan aurenta da wuri zai zo ta sa ta kullum shiga kitchen. Samun kanta tayi da tsoron kada yazo yaci abincinta taji kunya. "Uncle ba fa sosai na iya ba" "Ni dai zanci a haka sai na tantance. Gobe ta nan zan biyo kafin na wuce in sha Allah. Ki hada min breakfast da kanki please" Tuni kwakwalwarta ta fara laluben me zata dafa. Ko dai tayi shiru ne kawai ta bashi na gidan tayi sai tace masa ita tayi? Hannunsa ya dan kada a gaban fuskarta ta dawo daga duniyar tunanin. Plate din ya karba ya ajiye sannan ya kama hannuwanta duka biyu ya rike sosai a cikin nasa. Wani taushi yaji har baya son saki. "Jiya kinji duk yadda mukayi da Gimbi a waya ko?" "Kayi hakuri Uncle Allah na zata kaine ka kira" ta fada a dan tsorace don yana daga cikin abin da ya hanasu tun suna kanana yana zuwa gidan. Yace jin hirar wasu da bai shafeka ba babu kyau. "Na sani Umm Ruman. Amma idan kika sake jin irin haka kiyi saurin kashe wayar. Kinga jiya da kyar na iya bacci saboda nasan kinyi kuka" Bai ma gama ba yaga idon ya cika da hawaye. "Kada kiyi min kuka mana Princess." Ya girgiza kansa. Hawayen ne kawai ya zubo ba shiri Awaisu ya tattarota gabadaya ya dorata akan cinyarsa yana shafa saman kanta. Bakinsa dai bazai iya fassara yadda yake ji ba a lokacin. Itama duk da bata gama gane me take ji akan Uncle Awaisu ba kunya mara misaltuwa ce ta kama ta. "Nayi zaton Umm Ruman dina jarumar mace ce wadda abu irin wannan ba zai sa naga ragwantarta ba" Hawayen ya goge mata da yatsansa ta rinka sunkuyar da kai. Suna haka wayarsa tayi ringing. Kamar ya share don baya son komai ya shigar masa dan lokacin da yake dashi tare da Rumana. Sake kira akayi yaga sunan Harisu ne sai ya dauka. Rumana tayi ta kokarin zamewa daga jikinsa ganin hankalinsa ya tafi kan wayar yayi mata wani riko da hannu daya wanda yasa dole ta hakura. Tsoronta kada wani ya shigo ya gansu a haka. Ina zata saka kanta idan haka ta faru. Bayan ya gama wayar yana rike da ita suka mike tsaye amma fuskarsa ta canja. "Zan je gida Yaya yana nemana. Bansan dai ko menene ba amma yace min kowa lafiya yake" Yadda yake magana Rumana ta gane hankalinsa a tashe yake. Gabanta har yana faduwa ko Maamu ce. Shima ya kula nata hankalin ya soma tashi yace ta kwantar da hankalinta babu komai in sha Allah. "Uncle ko na raka ka?" Tayi maganar da karamar murya. Tausayinsa take ji amma bata son fadin abin da zai zama tayi rashin kunya. Tasan dai da bata aure shi ba zata dage sai ta bishi ne. "Kiyi zamanki zanyi kokarin dawowa anjima don bamu gama hirar ba" Fitowa yayi yayi yayarsa sallama ya tafi ita kuma ta kwaso kwanukan da yaci abincin. ***** Dakin Maamu ya wuce kai tsaye. Zuciyarsa ba karamin bugu take yi ba kafin ya karaso gidan ko jikinta ne. Yana daga labulen dakin wani mummunan wari ya daki hancinsa. Hannu yasa ya rufe hancin yana kallon su Harisu dake zaune a wurin kowa ya toshe hanci. Da kyar ya iya hadiyar yawu yace "warin meye wannan Yaya?" "Ka tuna ranar da Maamu ta dage a sallameta da Dr. Yana tace ta kama Gimbi zata shafa mata wani abu?" "Eh" ba sauraren Harisu yake sosai ba tunda idanunsa suka gane masa abin dake warin. Wani abu ne kamar izgar doki amma daga kasansa yana da kauri sosai. Ta wurin kaurin ne wani irin ruwa mai wari ke fita. Abba da yake dakin ya daure ledar ya fita da ita sannan Harisu ya cigaba da fada masa ko menene abin. "tun safe Dr. Yana ta kirani wai idan ina da lokaci naje asibitin. Nace bani da halin zuwa to sai Allah Yasa Abba bashi da komai a makaranta yau shine na tura shi. Wannan abin da ka gani shine Gimbi taso shafawa Maamu kwanaki. Wai kwana biyu kenan suna jin wari daga harabar dakin da Maamu ta kwanta an rasa ko meye. Sai da safe yau wani mai shara ya gano shi da alama ta taga aka jefa." Gaban Maamu Awaisu yaje ya zauna ya rungumota yana hawaye itama tana yi. Wace irin masifa ce Gimbi take bibiyarsu da ita. Wato har a gadon asibiti bata kyale masa uwa ba. Duk wani dan guntun tausayinta da yake tunanin akwai ko zai iyaji a gaba a take ya fice masa daga rai kamar sauke dutse mai nauyi. Baaba ma kukan take yi bare ma da suka ga sunan Maamu barobaro a daidai inda warin yake fitowa. Abba da ya fita da abin Harisu da Awaisu ya jira suka fito suka tafi dashi can bayan gida aka kona. Haka Awaisu ya karasa wunin jiki babu kwari. Tare da Harisu suka yi sallar Magriba da Isha. Bayan sun dawo daga sallar Isha Baaba ta kira shi. "Awaisu wannan damuwar fa bazata chanja komai ba sai dora maka ciwo. Kayi hakuri tunda Allah Ya taimakemu bata sami nasara ba" "Baaba yanzu fa da ta tabata dashi kila ko kallon Maamu bazan sake ba. Wai me Gimbi take nema ne a tare dani? Babu abin da na rage yi mata saboda zuwan su Maamu Abuja" Baaba tayi dan murmushin takaici "baka san mata ba kenan. Wasu a rayuwarsu su gansu da miji sai yadda suka ce shine babban burinsu. Akwai matan da suke kishi da surukansu. Kaga mace na kishi da matar da ko ita matar dan ta sa ido lallai duk abin da zakayi nata yafi na mahaifiyarka. Zamani ne yazo yanzu ayyukan sa6o sun yawaita. Wani abin idan kaji sai ka rasa ina hankulanmu suke tafiya. Saboda abin duniya da jindadi na takaitaccen lokaci sai mu koma tamkar jahilan farko. Ga addini amma bama aiki dashi" Kansa ne yaji har ciwo yake masa saboda tunani da damuwa yace "to ni yanzu yaya zanyi da su Haris? Gimbi mahaifiyarsu ce ina tsoron kada abubuwan da take yi suyi tasiri akansu su fara koyi da ita" Baaba tayi saurin daga hannu "Allah Ya kiyayemu mugun ji da mugun gani. In sha Allah Allah zai tsare musu imaninsu. Amma ina tunanin me zai hana ka kaisu gidan Alh Mudi kafin asan yadda za'ayi da uwar." Shawarar Baaba tayi masa yace in sha Allah zaiyi magana da iyayen Gimbi. Don har zuciyarsa baya so yana fita yana barita dasu. Su Maman Gimbin ma sun kira Harisu zasu zo ranar laraba. "Wai bazaka tashi ka tafi wurin matarka bane?" Baaba ta fada masa tana kallonsa da tausayawa. Duk ya zabge ma tun da aka fara case din. Agogonsa ya kalla ya dan dukar da kai "Baaba dare yayi ne. Kinga har tara saura. Wallahi abin nan ne duk ya tsaya min" "Allah Sarki idan damuwa tayi yawa ai babu inda ya dace da mutum sai wurin masoyinsa" tana magana tana dariya. "Da safe zan biya kafin na tafi" ba dai haka yaso ba shi da yazo musamman saboda ita. Dan daure fuska Baaba tayi "ai ni bansan dalilin da yasa kuka kulla tafiyarta gidan Ummukulsum ba. Banda ragon azanci tunda a nan zaka kwana ai sai ka fi samun lokaci tare da ita. Kira min yayar taka muyi magana. Sauran ma zamu hadu dasu su tsara yadda za'a danyi taron biki cikin wata mai zuwa ta tare" Wayar ya mika mata bayan yaji ta shiga. Tana dauka ta fara mitar me ya hana shi dawowa. Baaba ce ta soma labarta mata me ya faru sannan tace maza Rumana ta shirya yanzu zaizo ya dauketa. Ummukulsum tace ta yarda amma don Allah da safe a dawo da ita don akwai shirin da zata fara. Dama Awaisun ma ganin mijinta baya gari bai dace yayi musu zuwan dare ba haka shiyasa yaso hakura. Cikin minti shabiyar yayi saurin watsa ruwa ya shirya cikin kananun kaya ya fita. A can gidan Anti Ummukulsum kiran Rumana tayi tace maza taje tayi wanka tayi kwalliya amma ba mai yawa ba. "Anti wanka a daren nan kuma?" An katse mata kallon da suke yi da 'yan uwanta. "Maza ki shige kuma wallahi banda jika-jika. Kwalliya kuma yar kadan ta isa. Mijinki zai zo mayar dake gida amma gobe zai dawo dake kafin ya wuce." Ji tayi ana neman kulle mata kai. Ance tazo ta kwana yanzu kuma ta tafi ta dawo. Ba dai tayi musu ba taje cika umarni. Har Awaisu ya iso Rumana bata gama shiri ba. Shi da Anti Ummukulsum suka zauna yana bata labarin abin da ya faru. Itama ta kara jin tsanar Gimbi tunda bata ji kunyar idanunsu ba tazo raba da da mahaifiya. Dama tana son ganinshi game da Rumana. Dazu da zata ci tuwo ta kamata ta gutsira shi ta soya mai da yaji wai a haka zata ci. Dama gata ba wani jikin arziki ba musamman ga yadda yunwa ta kassarata. 'Yan sinadaran gina jiki duk babu isassu ga aure daga sama. Shawara ta yanke dole ta gyara 'yarta don wanda ya zauna da Gimbi sai mace tayi da gaske zata iya zama da mijinta. Magunguna da ake sha kuma ba wani tasirin arziki zasuyi ba matukar babu cima mai kyau. "Ango don Allah ina bukatar 'yan kudi na gyara amarya" "Kuna cewa angon nan kunya nake ji" yayi dariya. "tunda kunya kake ji to tashi ka tafi na fasa baka ita." "Tuba nake ranki ya dade. Yanzu dai nawa kike bukata?" "Duk abin da ya samu...amma fa ka saki bakin aljihu gyaran gaske zamuyi" Alkawarin taho mata da kudin da safe yayi domin a lokaci bashi da cash da zai isa ya bata. ***** Da sallama Rumana ta shiga falon. Ganin Anti Ummukulsum yasa tayi saurin juyawa zata gudu. "Dawo ke muke jira dama. Sai da safenku bari na shiga ciki." A bakin kofa ta rabe har Antin ta fito a hankali tace ta saki jikinta mijinta ne fa. Murmushi kawai tayi ta kutsa kai cikin falon suka yi karo da Uncle Awaisu yana fitowa. Janyota yayi da sauri ganin tana neman dafa bango kada ta fadi. "Gaskiya akwai matsala. Haka kike ba nauyi, yar wannan turewar tana neman kayar min dake" "Matsawa fa nayi don kada kace na tureka amma baka ji nauyina ba...." Sama taji yayi da ita maimakon su fito ya koma cikin falon da baya yana dauke da ita. Salati ta soma yi sai kuma ihu ya biyo baya saboda yadda taji yana neman juyawa da ita ta kankame masa wuya. Yadda take tsoron hajijiya saboda jiri shiyasa bata ko son ta ga anayi. Ihun nata da bai gama fita daga bakinta bane ya makale sakamakon bakinsa da taji akan nata. Wani irin yanayi suka shiga bare ma Awaisu wanda yaji gabadaya komai ya tsaya masa. Baya tunanin komai sai Rumana da soyayyar da yake yi mata. Da kyar ya iya kyaleta ya kalli fuskarta ta rufe idanu kamkam jikinta har wani rawa yake yi saboda tsananin faduwar gaba. A hankali ta bude idonta suka sauka cikin nashi tayi saurin kuma rufe su da taga kansa ya sake dukowa gareta. Wannan karon peck ya mata a goshi. "Kinji kunya ne Princess? Kada ki damu muna nan dake idan kika fara yi min son so da kanki zaki...." Duk da bata san me zaice ba amma bata son ji don ko da wannan kunyar ya barta tana ganin zata shekara bata dawo daidai ba a gabansa. Hannu tasa ta rufe masa bakin har lokacin yana dauke da ita. Shi ga tsaho ga jikinsa ba'a kira shi mai kiba ko siriri ba ita kuma ga kankanta ga rashin kiba. Wannan karon a tafin hannun taji ya sake mata wani kiss din ta cire da sauri tana salati. Dariya yayi ya sauketa yana rike mata hannun "Allah Ya hadani da ustaziyya" Hanyar fita yaga tayi yabi bayanta batare da ya saki hannun ba. Suna fitowa Anti Ummukulsum ta leko ta sama don taji shiru kamar basu fita ba ta gansu. Dadi ne ya cika mata zuciya tana addu'ar Allah Ya kara musu so da fahimtar juna. Rumana abar tausayi ce matsawar Gimbi tana gidansa sannan ga kuruciya bata san komai ba. Shiyasa dole ta gyarata don ta kara mata daraja a idon miji. ***** Da kansa ya bude mata ta shiga sannan ya shiga ya tayar da motar. Dan kallonta yayi duk ta takure kamar mai jin tsoronsa. Ya tallabo kansa yana kare mata kallo "Yau fa na janyowa kaina dama da kyar ake yi min magana gashi yanzu ko sannu da zuwa ban samu ba" muryarsa a karye irin abin tausayi dinnan. "To ba kaine ba..."ta turo baki kamar zata masa kuka. "Allah Sarki Princess nine nayi miki ki......" Hannuwanta tasa ta toshe kunnuwanta "don Allah kada ka fadi sunan" Ya daga gira daya "Au ashe ma kinsan ko meye " Cikin sauri tace "a'a ban sani ba" Dariya yake mata sosai yadda ta rude "To ki bari na fada miko ko da next time kina so kinsan me zaki ce min" Tace "Na sani" ya sake daga gira "Ban sani ba" tayi saurin gyarawa shi kuwa sai dariya yake yi mata ya manta fiye da rabin bacin ransa. Kafadunta ya dafa "I love you so much Umm Ruman. Duk da abu ne da wata uku da suka wuce ban taba tunanin zan wayi gari naga rana irin ta yau ba. Amma nasan cewa Allah ne Ya bani ke domin samun sassaucin laifukan da na aikata muku musamman Maamu da bani da tamkarta. Aurenki shine hanyar da tafi cancanta na faranta muku ke da ita. Please Princess ko yaya kiyi min son so dinnan kinji. Yanzu ni mijinki ne. Miji kuma yana taka rawa daban daban a wurin matarsa. Ni uba ne, aboki sannan masoyi gareki saidai na biyun da na ukun bazan iya nuna miki su sosai ba sai kin karbeni a sabon matsayin da Allah Ya hadamu" Idanunta cike da hawaye saboda maganganun sun shigeta muryarta can kasa tace "Uncle me ya sameka?" Yadda take turo baki haka shima yayi "yanzu na ajiye kunya na gama fada miki ina sonki shine zaki ce me ya sameni?" "Gani nayi kamar kana cikin damuwa lokacin da da na shigo kuna tare da Anti Ummukulsum" Mamaki ta bashi sosai. Yana rainata ashe wayonta ya wuce yadda yake gani. "Kin kawar min da damuwar tun dazu. Saura amsata " Ta rasa menene yake saka mata faduwar gaba yanzu a tare dashi. Tasan dai bata kinsa ko kadan amma wanna matsayin nasa na da yasa ta kasa sakewa har ta fuskanci me zuciyarta take ji game dashi. Gani take yi kunya da nauyinsa da wuya su barta. Amma bata so yaji kamar bata damu dashi ba. Dubi yadda ya rama mata zagin da Gimbi tayi musu. Wannam kadai ya zama matakin farko na canja yadda take ji game dashi. Yatsunta biyu babba da manuni ta hade tare da dunkule sauran ukun ta daga hannun a tsakiyarsu tana murmushi "In sha Allah" Ya kalli hannun ya kalleta "Umm Ruman me kenan?" Aha yau ta kure masa bai san me take nufi ba tace a ranta. Dariya ta soma yana binta da kallo cike da jindadi. Da kyar ta tattaro karfin hali tace "Uncle idan ka canki me haka yake nufi ...." Ya sake kallon hannun ta katseta "me zaki bani?" Dadi duk ya cikata ta sake sosai yau tayi abin da tasan da matukar wuya ya gano. "Abinci me dadi" "Kin ma isa...wannan aikin naki fa ba mai sauki bane da gani." "To me kake so?" Bakinsa ya nuna mata yana dariya a hankali. Shi da ba gwanin kallo ba saboda rashin lokaci tana ganin kamar bazau taba gane wani salo ne na cewa *I love you* ba da take gani a series din Korea da suke gani a dakin Abba. Karamin yatsanta ta daga shima ya biye mata ya saka nasa yatsan a ciki yace "Deal! yarinya ki shirya shan mamaki" Lumshe ido tayi harda dariya tana ganin tayi nasara.*KASHE FITILA*💡41 *Batul Mamman*💖 Kamar kada su tafi gida haka Awaisu ya rinka ji. Hanyar fita gari ya dauka Rumana ta dago kai a firgice. "Uncle ina zamu?" "Kin fiye tsoro Princess. Abu zan saya miki" Daga nan bai kuma magana ba har suka tsaya daidai wurin wani mai nama da yayi suna sosai a wurin. Murmushi tayi tana tuna lokutan baya kafin zuwansu Abuja. Babu zuwan da zaiyi garin bai tafi da ita da sauran 'yan uwanta siyan gasasshiyar kaza a wurin ba. Har kurar Awaisu babanta yake kiranta sai gashi yau sun kuma zuwa amma tana matsayin matar Awaisu. Tunani ne barkatai suke ta zuwar mata akan wannan sabuwar rayuwa sai da yayi kusan rabin awa ya dawo dauke da ledoji. A baya a ajiye sauran sannan ya shiga mazauninsa ya ajiye mata daya akan cinyarta. Zabura tayi tana kokarin mikewa tsaye ta ma manta a mota suke. Mamakin tashin nata yayi yace ta zauna. Cinyarta ya gani tana shafawa harda 'yar kwalla "Uncle ka kona min cinya" ta fada a shagwabe "Subhanallah" yace tare da kai hannunsa inda yaga tana murzawa. Kayan jikinta material ne mai santsi shiyasa taji shiga zafin har kanta. Hannun nata ya dauke kawai sai ta ga ya duka daidai cinyar yana hurawa. Tsigar jikinta taji ta tashi ta fara jan kafar yayi saurin rikewa. "Kiyi hakuri don Allah na manta da zafi na baki don kici yanzu" Ita dai so take ya kyaleta kawai tace "ya dena zafin ma" AC taga ya kara sannan ya dan hade fuska babu alamun wasa "bari na janye skirt din kisha iska sosai kafin mu isa gida" "Iyyeeee, a janye me?" Ta fada tana zaro idanu a firgice. Ya kama skirt din "nace ki bari yasha iska kuma na ga yadda wurin yayi. Kada yaja ruwa ko tabo" 'Yar dariya ta soma yi wadda bata boye tsoron da yake bayyane a fuskarta ba "Lahhhh ashe ka zata gaske ne naji zafi...to wasa nake yi kawai." Dariya yayi wai kamar shi zata yiwa wayo. Tsoron da ya gani tattare da ita yasa ya kyaleta. So yake ta soshi ba taji tsoransa ba. Motar ya tayar suka kama hanyar gida yana satar kallonta tana sosa wurin. Da ta ga ya juyo sai ta dauke hannunta da sauri. Wani chemist ya tsaya ya sayi magani suka wuce. Cikin kannenta ya kira wani mai suna Jamal ya bashi ledoji biyar manya cike da naman kajin nan yace ya kai ciki a raba musu. Shi kuma ya dauko leda uku a hannu ya zagayo bangarenta ya dauki nata. "Muje na kaiwa su Maamu nasu sai na shafa miki magani" "A ina? Wanne?? Maganin meye???" "Bana son musu ki wuce muje kawai" ya fada tare da yin gaba. Jikinta a sanyaye tabi bayansa. Ta yaya zai shafa mata magani a cinya. Shi ko kunyarta ma baya ji. Ita ce fa Rumana! Dakin Maamu suka fara zuwa har tayi bacci. Ya bude fridge zai saka Rumana ta karbi ledar tace bari ta cire albasa da kabejin da yake ciki kada ya bata naman idan ya kwana. Kamar yadda Hajiya Umma yayar Mama ta fada mata komai tayiwa mahaifiyarsa zai kara mata kima a idonsa haka ta kula da yadda yaji dadi sosai. Jiranta yayi ta cire sannan ta saka a fridge din suka tafi wurin Baaba. Ga dukkan alamu itama baccin take shirin yi. Fuskarta a sake da ta gansu dadi ya mamaye mata zuciya. "Awaisu kai da kake da tafiya a gabanka gobe shine baka yi shirin kwanciya ba?" Leda daya ya ajiye mata yana murmushi "nama na tafi nema miki Baaba" "A'a wannan kurar dai ta kusa da kai ka sayawa na sani." Ta bude ta dauki daya tana dariya saboda Rumana tace ita ba kura bace. "Yaya ya shigo ne?" "Bai dade da tashi ba. Dama maganar tarewar Rumana ne. Kana ganin nan da sati hudu masu zuwa yayi maka? kada ta rasa da yawa a karatunta. 'Yan uwanka suna son su kammala shirye shirye don ko tsinke ba'a fara tanadar mata ba" Zama yayi sosai Rumana zata fita yace ta zauna itama. Baaba Hure ya kalla sai kuma ya dukar da kansa. "Yanzu Baaba ni Yaya Harisu zai yiwa haka? Ko ban auri Rumana ba waye zaiyi mata kayan daki idan ta tashi aure?" Baaba ta dan murmusa "kai ne." "To wallahi bana bukatar komai daga wurinsa. Ban isa na rama muku komai da kuka min ba Baaba. Bani da wannan niyar ma. Amma burina bai wuce na ga na kyautata muku iya yadda Allah Ya bani iko. Banda al'amura sun zo mana a haka Rumana a gida ya kamata ta zauna har aurenta. To kuma yadda nasan da hakan ta faru bazanso kowa yace zai shigar min kan maganar kayan daki da abubuwan da amarya take bukata ba yanzu ma bana so. Kawai ku saka mana albarka shikenan" Baaba ta share kwalla "Awaisu meye baka yi mana ba? Yayanka da mazan yan uwanka mata babu wanda baka karawa jari ba. Yaransu duka babu wanda baici moriyar samunka ba. Duk wata aike baya yankewa tsakaninmu da kai ko da baka zo garin nan ba. Me zamu ce maka mu kuwa. Allah Ya kara yi muku albarka Ya rabaku da dukkan sharri" Suka amsa da amin. Satar kallonsa Rumana tayi tana murmushi hannunta na daidai wurin kunar ta ma manta ta dan sosa wurin. ""Ya soma kaikayi ne?" Baaba tace meye yake kaikayi kuma. Cinyar Rumana ya nuna mata tare da bayanin me ya sameta. Saman wardrobe dinta ta nuna masa. "Ga zuma can dauko ka shafa mata kada ya tashi. Kasan ba'a raina kuna." Rumana ta tashi har tana tuntube da kafar Awaisu. "Bari na dauko naje daki na shafa" Baaba ta wurga mata wata uwar harara "kin sami wuri kin zauna ko kuwa. Dauko kaji dan albarka" ta yiwa Awaisu murmushi. Dariya yayi yadda Rumana tayi kicin-kicin da fuska kamar zatayi kuka. Shima kuma da ya dauko sai ya kalli Baaba a dan kunyace ya mikawa Rumana kwalbar zumar. Duk abinsa da kunya ya kwaye mata cinya a gaban kakarta. Baaba ta kada kai "Ahaf, abin da yanzu aka fara auren. Meye a shafa zuma mu da za'a kawo mana 'yan dugwi-dugwi mu goya. Indai don nice ku kara gaba don ba fita zanyi na bar muku dakin ba." Kafin ma ta kai karshen maganar Rumana ta fice da sauri Awaisu ya bi bayanta yana dariya. Ita kuwa Baaba suna fita addua take Allah Ya kara hada kansu. Da kyar ya kamota zata yi hanyar dakin mamanta. "Wannan sauri kamar zaki tashi...ga wannan maganin shima na shafawa ne. Ki bara shafa zumar yau gobe sai kiyi amfani dashi. Ga naki naman kici kafin ki kwanta. Lastly kuma kada ki kashe wayarki zan kira" Juyawa yayi ya tafi ya shige dakin Mama. Bata yi mamakin ganinta ba don taji sanda Baaba Hurw ke fadawa Maamu wai yaran yanzu basa lissafi. Ji dai Awaisu da Ummukulsum wai sun kai Rumana can gidan bayan a nan zaifi ganinta son ransa. Ko da suka fara zancen Mama fita tayi don kunya suka sa taji. Nata naman ne a gabanta tana ci tace yanzu aka raba aka kawo mata. Rumana duk kunya ta isheta ta shige uwar dakin ta dauko charger ta tafi nasu dakin bayan tayi mata sai da safe. Wayar kusan awa daya sukayi kafin sukwanta duk da shine yake kaso casa'in na maganar. Tun da tayi asuba bata koma bacci ba ta zauna gari ya danyi haske tayi wanka ta shirya. Takwas da mintuna kadan ya kirata yace ya shirya ta fito ya kaita gidan Anti Ummukulsum ya wuce. Sai a lokacin yake danasanin kin tahowa da drebansa. Harisu ya fito sunyi sallama yaje wurin Maamu suka taba hira tace yaushe zai dawo yace Juma'a. Ai kuwa ta rinka dariya tana cewa ya hakura sai nan da wata biyu ita ta warke. Yadda yayi mata da fuska ya kara bata dariya. "Wasa nake maka angon Rumana" Ya dan sosa keya "Maamu harda ke a tsokanar" "Nice ma kan gaba." Ta gyara zama "Ka kula da amanar Rumana kaji ko. Kada naji ko na gani. Idan wancan karon tsautsayi ya ritsa damu sake faruwarsa sunansa sakaci daga gareka. A wannan lokacin kuma zan nuna maka fushina" "In sha Allah bazan taba ganin fushin nan ba kuwa Maamu. Zan rike miki ita tsakani da Allah" "Haka nake son ji. Allah Yayi albarka Ya tsare hanya Ya kaika lafiya. A kiyaye haram komai kyau da dadinta halaka ce" Yaji dadin adduar sosai yayi sallama da kowa ya fita sannan Rumana ta fito don kunyar biyo bayansa take ji gaban mutane. Gaishe shi tayi sanna ta shiga ta zauna. Kallonta ya rinka yi tayi kyau duk da hijab ne ma a jikinta. Sun fara tafiya taji hannunsa akan cinyarta. "Kin hanani jinya bayan ni na jawo ciwon. How do you feel yau?" Kunyarsa ta yau har tafi jiya saboda hasken gari yana ganinta sosai. Da kyar ta amsa masa. Bakin ATM machine ya tsaya ya ciro kudi suka tafi gidan Anti Ummukulsum. Da sauri sauri suka gaisa don yace baya son tafiyar dare. Dubu dari ya bata yace tayi masa magana idan bai isa ba. Rumana ya nema har ta tafi wurin Iman aka kira masa ita. Su biyu ne a falon da suka zauna jiya. Idonsa a kanta yace "kin tuna me ya faru a falon nan jiya?" Wayyo tace a fili tana rufe ido. Haka zata zauna dashi yana sata jin kunya haka. Yaushe zata manta ita kuwa. Tashi yayi tsaye "ban manta assignment din da kika bani ba. Ki shirya ina dawowa zaki cika alkawarinki kema" "Bafa alkawari nayi ba Uncle" "Har kin karaya kenan. To ki kwana da saninki ina dawowa zaki biya da abin da na fada miki jiya" ya dan daga kai ita kuwa sai ta juya gefe. "Zan tafi Umm Ruman babu ko sallamar miji da zan samu? " "Uncle Allah Ya kiyaye hanya Ya kaika lafiya" "Amin amma sauran wannan" Hannuwansa taga ya ware alamun tazo ya rungumeta. Sakin baki tayi tana mamaki. Ko da wasa bazata iya ba. Hannunsa ya kuma nuna mata da kansa yana jiranta. "Zaki sa nayi dare fa. Ni fa babu inda zani sai kinyi min irin sallamar da nake so" Tsaye take tana ta shawarar me zatayi. Uncle Awaisu ya sakata a tsaka babu mafita. Tana dago kanta suka sake hada ido ya kyabe mata fuska shi ya gaji. A hankali ta rinka takowa gabansa. Har ta kusa karasawa cikin hannuwansa yana murmushi sai kawai yaga ta zagaye ta bayansa ta rungume shi a hakan ta hanyar zuro hannuwanta ta karkashin nasa ta kwantar da kanta a bayansa. Motsin kirki Awaisu ya kasa saboda yadda yaji. Yatsunsa ya zura cikin nata masu dauke da jan lalle mai kyau yana ta murmushi ya kasa ce mata komai. Rumana ta gama masa komai ta shige ko'ina a cikin zuciyarsa. Tsoron abinda zai iya biyo idan ya kalleta yasa bai juyo ba sai hannunta da ya dan matse sannan yace "Kamar kullum ki kular min da kanki. Ina yi miki son so Umm Ruman. Wannan new way of saying I love you ne" Daga bayan nasa tayi wani kyakkyawan murmushi cike da kunya ta sake shi. Wai Uncle Awaisu yana sonta. Shima bai juya ba ya yi gaba yana kara jin sonta ya wuce. ****** Bayan tafiyarsa Anti Ummukulsum ta kirata daki. Plate ta miko mata ta kalli abin ciki ta kasa tantance ko menene. "Daga yau kada na sake ganin kina cin komai sai abin da na baki kina jina. Wannan kasusuwan nake son rufewa kafin ki tare. Kuma kina bukatar kayan gina jiki don haka kada na kuskura wallahi na kamaki da kayan kwalamar da kuke ci da Iman." Rumana tayi murmushi "To Aunty meye wannan din?" "Zogale ne na dafa na soya soya da albasa mai yawa da tumatir da kwai. Kici kisha wancan youghurt din" ta amsa mata. Rumana ta ja plate tana kwasar dadi. Daga ranar Anti Ummukulsum ta dauki damarar gyaran 'yarta. Kullum sai tayi mata farfesun kaji, kifi, kayan ciki ko nama. Ganye kuwa wasu ko sunansu bata sani ba haka take yi mata miyar tuwo ko farar shinkafa. Ga maltina sai tasha gwangwani hudu a rana. cikin dan kankanin lokaci ta soma canjawa ita kanta tana ji a jikinta. ****** Washegarin komawar Awaisu yaje gidansu Gimbi ya sanar da iyayenta zai kawo su Daula na dan lokaci. Mama tace dama taso tayi masa magana tun ranar da yazo ma. Sun sanar dashi lokacin da ya tashi komawa Fika ya fada musu tare zasu je. Gidan nasa kuma a lokacin suka bi bayansa zasu taho da yaran su ga Gimbi. Suna ta sallama ba'a amsa ba yana daga bayan Alh Mudi yace su shiga kawai yaran suna islamiyya ne. Mama kai tsaye dakin Gimbi ta wuce. Waya take yi ma bata ji shigowarta ba tana ta fada sai sakin kudi take yiwa su Ovi a kaiwa boka amma babu wani chanji. Ganin Mama yasa ta tashi da sauri ta katse wayar. "Mama yaushe kika shigo?" "Fito falo babanki yana jira" Gabanta ne ya fadi. Rabonta da shi tun lokacin da Awaisu ya saketa taje gida. Dankwalinta ta janyo ta daura ta fito. Ganin Awaisu a wurin yasa tayi wani dan murmushi, wato ta nan ya bullo kuma. "Alhaji sannu da zuwa, Abban Haris yaushe ka shigo?" Ta fada fuska a sake. Alh Mudi ne ya soma magana "kinga bana son gulma ki zauna kawai muyi abin da ya kawo mu. Duk abubuwan da kikayi Gimbiya mun sami labari. Wallahi kin bamu kunya amma ki sani ba kowa kika cuta ba sai kanki." Kuka ta soma yi "Alhaji sharri yan uwansa suka kulla min don kawai basa sona. Zancen da nake muku fa 'yar yarinyar nan da na rike suka aura masa" Mama tace "Allah Yayi musu albarka da wannan hadin. Gimbi kada ki manta Bebi kanwata ce saboda haka idan ma kina shirin wani rainin hankalin ne ki nemi wanda zakiyiwa ba mu ba. Awaisu da danginsa bazasu miki sharri ba domin idanuna sun gani tun kafin ma Maamu ta dade a gidan nan kika ce min ba haka ba." Alh Mudi ya karba "Jiya muka dawo daga wurin Inna (babarsu Mama da Anti Bebi). Rokon su Amina gafara take akan yadda ta juya musu baya komai sai Bebi. Tayi rantsuwa bata san lokacin da take wasu abubuwan ba musamman danne musu hakki da Baba ya rasu da ta hada kadarorinsa da dama ta bawa Bebi a boye. Abin da ya rage aka raba daidai kuma da ita. Ke bari na takaice miki a yanzu Bebi da mahaukaciya fa bambancinsu bashi da yawa. Idan bazaki tub.... " Murmushi yaga Gimbi tana yi wanda ya bayyana tsantsar farincikinta jin ance Anti Bebi ta zama kamar mahaukaciya. Abin ya konawa Mama rai ta kai mata duka. Haka suka zauna suna ta nasiha da fada yana bi ta bayan kunne. Da suka tafi ta tashi harda kade riga tabi bayan Awaisu. "To me zuciyar yara a karo na karshe ina fada maka ka barni na fita daga gidannan kafin ka ga ba daidai ba" Yana zare necktie dinsa yace "na nawa kuma. Kada ki damu kwana nawa ne zaki kara gaba" Tsoro ne ya kamata don har mamaki takeyi wani azababben so da take masa yanzu. Duk wannan ruguntsimin da suke fama dashi son Awaisu karuwa yake a ranta kamar ana hura wuta 'yan kwanakin nan. Da farko neman mafita take ko dai zamansu ya gyaru ko kuma ya saketa. Yanzu kuwa ido rufe gyaran take nema. Haka ta fita ba don taso ba. Har juma'a ta zagayo suna faman rigima tana son fita ga yaranta an kwashe sun koma gidan iyayenta. Wannan abu ma yayi mata ciwo. A cikin kwanakin bashi da nutsuwa sai idan yana waya da mutanen Fika musamman amarya Rumana. Daga banki sai gida yake zuwa. Bincike yake yi akan wadanda Gimbi ke muamalar zuwa wurin yan tsibbu tare dasu. Abin da Gimbi bata sani ba shine kwanaki uku da suka wuce Anti Bebi da kyar da sidin goshi Wangesi ya yarda ya ganta. A nan ne take fada masa cewa tana zargin Gimbi domin aljanu har magana suke mata a kunne suce Gimbi tafi karfinta gashi sun jawo ana ganin kamar bata da hankali. Bayan dogon bincikensa na tsafi ya gano gaskiya ta fada. Fushi yayi mai tsanani har yaushe Gimbi ta isa tayi masa wasa da hankali. A dalilin haka yayi alkawarin ko me Anti Bebi take so ayi mata zaiyi. Shine ta rokeshi ya cusawa Gimbiya soyayya da kishin Awaisu na fitar hankali. Irin son da ko macen kuda bataso ta rabe shi. Ita kuma zata je ta tona mata asiri ya saketa. Tasan wannan son shine zai zamewa Gimbi masifa a duniya. Ko babu asiri mahaukacin son da take masa ne yasa bata son kowa ya rabesu musamman uwarmiji kada asa shi ya saketa. ***** Dan sakin fuska yau ta shiga dakinsa tana tsaye daga gefen mudubi shi kuma yana ta aiki "kasan dai ina da hakki a kanka ko Abban Haris. Yaushe rabonka da zuwa inda nake?" Tafi ya rinka yi har ya isa gabanta "amma dai baki da kunya Gimbi. Wai hakkinki. To na karfine sai ki kwata ko kisa bokanki ya baki tunda dashi kika dogara." Ranta a dagule ta soma fada "nifa bazaka dokeni ka hanani kuka ba. Ka rufe ni a gida babu fita sannan ka tauye min hakki. Ga waccan shshh....." Babu yadda za'ayi ta karasa zagin don wani mugun kallo yake watsa mata. "Kina iya fita gobe duk inda zaki kada ki wuce karfe hudu ki dawo gida." Taji yace Anya kunnenta ya jiye mata daidai kuwa? Bata son jan zancen kada yace ya fasa tace to kawai ta fita. A baya ya bita yana jikin kofa yaji tana waya tana cewa zata zo gobe. Dariya yayi ya koma daki. Ya rasa yadda zaiyi ya dauki wayarta saboda balain yadda take kaffa kaffa da ita ko bandaki ta shiga idan ya duba dakin baya gani. Ba dai haka yaso ba amma dole ya kira Rumana ya bata hakuri na rashin zuwansa a satin. Dama ita da take jin kunyarsa sai ta nuna bata damu ba har yana ta mita wai taki fara yi masa son so har yanzu yana so ta fara shiri tarbarsa sati mai zuwa. Washegari kafin tara na safe Gimbi ta fita don ko ganinta baiyi ba. Yana fitowa daga daki da yaga bata nan ya koma yayi alwala tare da nafila raka'a biyu don neman kariya. Dakin Gimbi ya fara shiga ya fiddo kayanta daga wardrobe ya bincikesu. A ciki ya tsinci layu da guraye sunfi goma. Karkashin gado, kasan kafet har su toilet babu inda bai duba ba. Abubuwa ya rinka gani harda wasu irin ruwa masu kala a robobi. Jikinsa sosai yayi sanyi karshenta babu wanda baa zuba masa ba. Yana gamawa da dakinta nasa ya koma shi kam har cikin pillow da kasan katifa akwai ajiyar layu. Haka ya wuni yana wannan aikin harda su kitchen, dakin Maamu da duka dakunan baki da na yaransa. Bayan ya gama hadasu ya fita duk inda babu interlock a gidan yace maigadi ya tayashi tonawa. Yawanci duk wuraren shuka ne amma sunyi sa'a babu komai a wurin. Ciki ya koma duk yayi gumi ya watsa ruwa ya gyara dakinsa sannan ya kira cikin yaran shagonsa yace yazo yana nemansa. Kayan gidan kaf banda na dakin Gimbi amma komai harda kayan kitchen yace a samo dillalai masu saya saboda da yawa basu tsufa ba. Kafin ya tafi suka shawarta ina zaije wurin kayan furniture masu kyau. Sunan wani shago ya bashi a wata babbar plaza. Zama yayi yayi dogon list na abubuwan da zai saya nasa da Rumana da yaransa. Kayan kitchen da su labulaye da komai ya gama tsarinsa. Kudi dai zasuyi ciwo amma yadda ya tsorata da kayan tsafin nan ko bai kara aure ba ya zama dole ya rabu da komai na gidan domin samun kwanciyar hankali. Yaron shagon sai da yayi kusan awa daya ya dawo gidan tare da masu ganin kaya. Babu bata lokaci sukayi ciniki suka turo motocin dibar kaya. Gimbi na dawowa wurin karfe shida ta ga gate a bude motoci biyu manya cike da kaya suna fita. A gigice ta shiga gidan ta sami Awaisu a falo ya zuba hannuwa a aljihu yana magana da wani cikin mutanen inda yace duk da yasan zasu chanja kujerun amma suyi hakuri ya farke dukkansu ta kasa. Kasa magana tayi jikinta na bari tana tunanin ba dai ya ga ajiyar da tayi masa a daki ba. Ko da ta shiga nata dakin haka ta sami kayanta watse ko ta ina. Zama tayi jiki babu kwari ta dago jakarta tana tunanin ta ina zata zuba masa wannan maganin da akayi mata alkawarin karshen duk wata damurta yazo indai yasa shi a bakinsa.*KASHE FITILA*💡42 *Batul Mamman*💖 _Allah Ya tabbatar da alkhairi Ya baku hakurin zama da juna da zuri'a dayyiba. Alhamdulillah_ 💝 *U & H* 💝 *Its your dayyyyy* Aiki su Awaisu sukayi tukura ranar sai bayan isha suka tafi zasu dawo dibar sauran waahegari sannan shima zaije duba kayan da zai siyo. Dakinsa ya wuce babu komai sai barguna da ya shimfida a kasa don hatta pillowas yayi waje dasu. Kayansa kuwa da takardu wasu suna cikin akwatuna wasu ya turasu gefe a dakin. Wanka yayi ya kwanta bayansa har ciwo yake masa saboda tsabar gajiya. Yana jin yunwa amma baya tunanin zai iya fita daga gidan saboda ciwon jiki. Wayarsa ya dauko yana ta binciken aikin da Rumana ta bashi har yau ya kasa gane me take nufi. Zuwa yanzu ma dai gani yake ko kawai tsokanarsa tayi. Murmushi yake yi shi kadai idan ya tuna rabuwarsu. Bugu yaji a kofar dakin kamar daga sama ana yi da karfi. Sai lokacin ya tuna ya rufe dakin da mukulli da zai shiga wanka kada tazo ta saka masa wani abin a cikin kaya don ya tabbatar tunda ta fita babu abin da zai hanata dawowa da wani maganin. Tashi yayi ya bude mata ta kura masa ido. Yanzu komai nasa kyau yake mata fiye da yadda ta saba gani. Haushin kanta take ji sosai na wannan makauniyar soyayya da bata yi ba ko da can da kuruciya da ta tabbatar ta so shi sosai. "Naga an fitar da kusan komai na gidan nan banda dakunan baki da nawa" "Sababbi zan siyo ai kinsan nayi aure ko? To amaryar ce zata tare nan ba da dadewa ba" yana magana yana kallon hannuwanta da take kokarin taba shi dasu. Ja da baya yayi ya hade fuska ta sauke hannun ba shiri. "Ba zuwa nayi ka fada min bakar magana ba mijin Rumana mai budurwar zuciya. Nazo yi maka tuni ne akan kayan fadar kishiya da ban ga kana da niyar yi min ba tunda kayan dakina banda hargitsawa ko tsinke baa dauka an fitar ba" Yatsansa ta ga yana kadawa a gefen kansa "Gimbi kin fara shaye shaye ne? Ni kike tambaya kayan fadar kishiya? Idan har sai na baki zaki saka kaya to ki fara shirin yawo tsirara. Ke bari na fada miki wannan hannun da kika shafowa kayan tsibbunki idan kikayi gigin tabani dashi sai na karya shi. Sauran tarkacen da kika ajiye a lunguna da sakon gidan nan ma na konasu gabadaya kuma in sha Allah kin gama samun nasara a kaina da 'yan uwana na." Borin kunya ne ya kamata amma dayake ta kware ta daga kai tana hura hanci "ni ba damuwa zanyi da sharrin da aka cusa maka yarda dashi daga gidanku ba. Idan ma ka tsinci wani abu baya wuce wanda aka bawa Rumana ta binne a gidan nan don ka aureta. Kuma gashi bukatarsu ta biya sai su zuba ruwa a kasa su sha" "Kinga na gaji idan kin gama abin da ya kawoki sai anjima" kofar ya janyo ya rufe ya barta a tsaye daga waje. Shu'umin murmushin da yanzu take yi idan ta sami nasarar aiki tayi ta juya ta tafi. Indai itace sai ya dawo bata hakuri don tun kafin ya bude kofar ta shafa maganin a jikin hannun kofar dakin. Fatanta idan ya taba yaje ya dauki wani abu yaci da hannun ta samu maganin ya shiga cikinsa. Sai bayan wurin rabin awa da tafiyarta ya bude kofar ya fito rike da karamin towel jike da ruwa. Bismillah yayi ya goge kofar tun daga sama har kasanta. Duk da bai ganta ba amma yaji a jikinsa yanzu ko ta wane hali Gimbi zata yi kokarin hadashi da magungunanta. Ji yayi kamar ya saketa tun yanzu sai ya fasa. A kalla ta zauna ko na wata daya ne da Rumana ta kwashi guzurin bacin rai ta tafi dashi. Rumana ya kira Iman ta dauka tace masa tayi bacci. Ya kula tana kwanciya da wuri shiyasa yake kiranta da farkon dare. Yau da bai kira ba ta sami kanta da jiran wayar tasa har bacci ya dauketa. Gashi ita kuma tana kunyar kiransa da kanta. ***** Washegari Rumana da wuri tayi wanka saboda Mama tayi mata waya tace taje gidansu Hajiya Umma tana kiranta. Tana shiryawa Iman tazo ta zauna a kan gado "Rumana kina kiran Uncle Awaisu kuwa?" Ta madubi ta kalli Iman din "bangane ba?" "Naga kullum sai dai yayi ta kiranki a waya. Jiya ma ya kira kina bacci. Ke ko dan text dinnan bana jin kina masa bare su chatting a whatsapp." Juyowa tayi da kyau ta kalleta "Iman, Uncle ne fa. Sai in yi masa text don rashin kunya." Dariya Iman din ta yi taje ta kamo hannunta suka zauna "Jiya Ummanmu ta tambayeni ko kina masa waya nace kuna waya dai don ban san dalilin tambayar ba. Shine tace in fada miki ki rinka sakin jiki dashi gidansa zaki koma. Kuma dai Rumana baki gani mu masu samari ma ko babu kudin kira mukanyi text balle ke da mijinki. Mijin ma kamar Uncle dan gayu dan boko" Rumana tayi shiru jikinta ya danyi sanyi "tsakani da Allah ina son yi amma tsoro nake ji kada ya fassarani yace sonsa nake yi" Wani mugun duka Iman ta sakar mata a baya saki kara tare da mika hannu tana shafa wurin. Iman tace "Wai kada yace kina sonsa. To da bazaki so shi ba bayan ya zama mijinki? Ko don kinga babba ne" ta kare da sanyin jiki. Kuka Rumana ta soma yi mata ta girgiza kanta "kunyarsa kawai nake ji har cewa yake yana sona Iman. Idan ya fada sai naji har tsigar jikina na tashi. Wai ni yake so. Ta yaya zamu zauna idan aka kaini Abujan? Don bakiji yadda gabana ke faduwa ba." Duk da Iman ba wata babba bace amma tafi Rumana wayewa ta wannan fannin "ina jin fa kema kin fara sonsa ne tunda kike jin haka. Ki rinka yi masa text ko waya kice gaisheshi zaki yi zaiji dadi." "Idan nayi niyar yin abu sai naji tsoron kada yace bani da kunya ko kuma idan banyi ba yaji babu dadi. Shiyasa cikin biyun nake zabar rashin yin" "Cikin kudin da ya aikowa Ummanmu da tace yace a baki ki karba kisa kati mana ki kirashi" "Ya saka min kudi yafi 5000 a ciki shiyasa nace mata ta barshi bana bukata" Harararta Iman tayi "kina da wannan kudin shine kika gagara kiransa. To yanzu kafin ki fitan nan tura masa text na gaisuwa kawai" Da taimakon Iman ta rubuta text don duk wanda tayi sai Iman din tace baiyi ba. Karshe tambayarta tayi ko tana missing dinshi. Murmushi Rumana tayi ai kuwa Iman ta rantse sai ta rubuta tunda abin da ke ranta kenan. Tana turawa ta kashe wayar ta saka a yar jakarta. Bata ma son jin me zaice idan har yin text din laifi ne gashi Iman ta sakata rubuta abin da batayi niya ba. ****** Yanayin gajiyarsa ta jiya ya sanya shi tashi a makare. Shima wayarsa maigadi ya kira ya fada masa masu kwasar kaya sun dawo. Umarni ya bayar a bude musu gate yana zuwa. Alamun sakonni text ya gani da yawa ya dan bude ya duba sunayen wadanda suka turo ko akwai masu mahimmanci sosai ya fara cin karo da suna *SS* wanda a haka yayi saving din sunan Rumana wato son so. Cikin sauri ya bude saboda yau ce rana ta farko da ta taba turo masa. _Uncle ka tashi lafiya? Yaushe zaka dawo ne? I miss you._ Ya karanta yafi sau biyar bakinsa ya kasa rufuwa saboda farinciki. Karshe dai screenshot yayiwa text din yasa shi a screensaver. Da ya kirata yaji a kashe yasan kunya taji shiyasa ta kashe. A gurguje ya tafi wurin masu kwasar kayan aka ci gaba da gyaran gidan. Gimbi na ganin shigarsa daki ta koma nata dakin tsabar murna harda tsalle tayi. Bokan Ovi bashi da wasa tasan indai anyi yadda yace bukata kuwa zata biya. Rabuwa tayi dashi sai dare bayan ya dawo daga zabar kayan gida da zai saya ta shiga dakin tayi kwalliya tasha turaruka tana zuba kamshi. Karar ruwa taji daga bandaki tasan wanka yake yi ta sami wuri ta zauna. Yana fitowa ya ganta. Dauke kai yayi ta danyi murmushi "Kaga ba fada ne ya kawoni ba. Magana nake so muyi" "Ina jinki" "Ba wani jan zance zanyi ba yarinyar nan da ko sunanta bana son fada nake so ka saki" Fuska ya saki ya ce "shikenan bukatarki?" Bokan nan ba dai iya aiki ba ta fada a ranta "sauran komai mai sauki ne indai ka saketa" "Miko min takarda da biro zaifi akan na tura text" Jiki na rawa tana sauri ta dauko masa takarda da biron daga cikin jakar da yake zuwa office da ita. A kasa ya zauna yace ta matso ta rinka gani. Da ta tashi harda shigewa jikinsa. _Ni Awaisu Kabir Fika na saki Gimb.._ Wata muguwar wawura Gimbi tayiwa takardar. Kafin ya farga ta nadeta ta cusa a baki tana tauna iya karfinta. Awaisu baiyi magana ba ta tashi a fusace ta fita harda buga kofar dakin da karfinta. Sai a lokacin yayi dariya don ya fuskanci abin nata ya soma zama hauka. Wato ta saka masa magani ne nan a tunaninta yayi aiki a kansa. ***** A can Fika kuma da Rumana taje gidan kakaninta nasiha suka yi mata sosai da shawarwari akan zaman gidan miji tunda abu ne yazo musu duka babu shiri. Anti Umma tata shawarar harda yadda zata kula da kanta da kuma canza salon yadda take gabatar da kanta a gaban Awaisu domin kuwa yanzu mijinta ne shi kuma wannan matsayin ya danne duk wata alaka da ta san suna da ita a baya. Wasu abubuwan dai ji take sun girmi tunaninta musamman da yake ita ba mai kwashe kwashen kawaye bace bata tashi da lallai sai ta koyawa kanta ilimin da komai dadewar lokaci indai mace tayi aure zai zo gareta ba. Anti Umma tace mata lokacin kunya ya kare tunda an shafa Fatiha, yanzu sai karatun yadda za'ayi zaman. Ranar a nan ta wuni sai yamma likis ta koma gidan Anti Ummukulsum. Bata jima da tafiya ba kayayyakin da dangin Mama suka tura kannensu biyu Kano su siyo suka iso. Yawanci kayan kitchen ne kuma sunyi kokari sosai don an mata siyayyar da ta dace duk da kurewar lokaci. Su Anti Umma ne suka kai kayan gidan Harisu a matsayin tasu gudummawar. Lokacin yake sanar dasu yadda sukayi da Awaisu akan yi mata siyayya. Anti Umma tace babu yadda zasu aurar da 'ya ko tsinke babu. Aure daban zumunci daban. Basa fata ko da wasa nan gaba wani abu ya taso gori ya biyo baya. ***** A hankali kowane bangare ya cigaba da shiri. Rumana tana can tana shan gyara a wurin Antinta. Awaisu kuma ya wadata gidansa da duk kayan bukata don har fenti aka sake yiwa gidan. Kayan kitchen ne Harisu yace ya dakata har sai an kawo wanda gidansu Mama sukayi don sunyi rawar gani kada ayi ta asara wurin sayan wasu. Gimbiya bata sake shiga sabgar Awaisu ba don ba karamin tsorata tayi da sakin da ya kusa auna mata ba. Yanzu jira take yi Rumanan ta iso gidan ai ba sai da Boka kadai zata iya sawa ta bar mata gida ba. Har nawa take da zata yi kishi da ita. Yau alhamis Awaisu ya tashi daga wurin aiki ya wuce gidan Alh Maitama. Sun dade suna magana da shi akan halin da Gimbi da Anti Bebi suka sakasu. "Babu abin da yake damuwa Mal Awaisu kamar kashewa Shuhada aure da tayi. Wallahi da mijin nata yazo gidan nan ya shiga wani irin yanayi. Kuma gashi saki uku ne" Awaisu ya jinjina kai. Mutanen nan sunyi nisa. Yanzu dole sai dai ta auri wani anyi mata katanga da masoyinta. Shuhadan ya nemi gani bayan sunyi sallama da mahaifinta. Sun gaisa a mutumce har yake bata labarin abubuwan da suka faru da Maamu har zuwa aurensa da Rumana. Baki da rike tana dariya "Kaga ikon Allah ko. Allah sarki Rumana yaushe zata tare muzo yiwa Gimbi dannar kirji?" "Sai ki taho da yan sanda saboda na tabbatar bazaku rabu lafiya ba" shima yayi maganar yana dariya. "Shuhada nagode sosai da taimakon da kika yi min duk da a lokacin ban san me yake faruwa ba. Kuma ina so don Allah mu cigaba da zumunci. In sha Allah har gidan nan zan kawo miki Rumana kafin kema Allah Ya kawo mana suruki musha biki. Alhaji yace akwai kaninki da zaku je gani ba don haka ba da na gayyaceki biki har garinmu" Murmushi tayi "in sha Allah zumunci yanzu muka fara. Sai dai batun aure sai dai zuwa nan gaba. Yanzu dai masters zan nema in sha Allah" ***** Ranar Juma'a yana ta murna zai je Fika da sun tashi sai dai wannan karon da dreba zaije saboda ya sha wahalar tuki wancan zuwan. Rumana tun da tayi masa text dinnan bata sakewa dashi sosai sai ya kyaleta yana jiran su hadu. Yau ma baiyi nasarar gano aikin nan da ta bashi ba gashi har ya kusa tafiya Fikan. Yayi ta browsing akan sign language bai ci karo da wannan alamar ba. Hakura yayi kawai yace zai sa ta fada masa da bakinta. Idan tsokana ne kuwa yasan maganinta don ta bashi wuya. Wurinsu Haris ya fara zuwa ya kaiwa su Mama kudi duk da basu karba ba yayi musu alkawarin yana gama gyaran gida zai mayar dasu. Sai dai ya kula suna jindadin gidan sosai kuma ga chanji sosai a yanayin tarbiyarsu. Daula ce mai tsiwa ya kula tafi kowa nutsuwa duk da ba wai ta dena wasa ko harkokinsu na yara ba. Anti Ummukulsum ya fadawa tun safe yana hanya bayan ya tashi daga aiki amma yana so tasa Rumana yi masa girki duk da bai fada mata ya taho ba. So yayi ta ganshi kawai. Da taimakonta Rumana ta dafa tuwon shinkafa da miyar taushe wadda aka sawa ganyen ugwu da alayyahu don tasan yana daga cikin abincin da yake so. Sai lemon kankana da apple mai dadi. Anti Ummukulsum ta tafi amsa wayar maigidanta shima washegari zai dawo Rumana tana cin cingam ta ciro shi ta sake dandana miyar a karo na barkatai. Miyar tayi mata dadi sosai amma sai taji kamar da dan tsami wanda dandanon cingam din bakinta ya saka mata. Fridge ta bude ta dauko soyayyen jajjagen attaruhu da albasa ta kamfata a cokali daidai yadda take jin zai daidaita miyar ta zuba cokali biyu. Ta sake debowa taji Anti Ummukulsum na tahowa tayi saurin ajiyewa don ita tace miyar tayi. "Rumana ba dai karawa kika yi ba?" A tsorace tace "yanzu zan zuba naji kamar da tsami" "Ba dole kiji tsami ba kina ta fama da cingam mai tsami sosai. Kunfi so kuji miya ana ci ana shhhh da baki. Kije kiyi wanka ki shirya ina jiranki yanzu" "Fita zamuyi?" "Zamu je gida ne amma kiyi sauri kada yamma tayi" Rumana ta tafi ta shirya tana saukowa ta ga Anti Ummukulsum ta hada kwanukan abincin a cikin wani kwando mai kyau. Kwandon tace ta dauko su tafi. Suna zuwa gidan da murnarta ta shiga dakin Maamu don tayi kewarta sosai. A guje ta shiga tana kiran Maamun. Kamar yadda ta saba fadawa tayi jikinta tana tambayarta yaya jiki. "Jiki da sauki Rumana ina maman taki?" Sai a lokaci ta kula ita kadai ta karaso. Ashe Anti Ummukulsum din ta tsaya a falon Harisu inda suke hira da Awaisu yana masa fadan yaki cin abinci. "Rabu dashi na amarya yake jira. Ta shige dakin Maamu bari nace ta kawo maka abincin" Harisu ya kalla yana yar dariya "Yaya anyi min izinin tashi" Harisu yace nan da sati biyu zaku bar min gida ni dai. Dafe kai Awaisu yayi ya fita yana dariya Anti Ummukulsum na tsokanarsu su biyun. Rumana tana jikin Maamu tana bata labarin kayan dadin da take ci wanda yayi sanadiyar chanjin da Maamun ta gani a jikinta. "Ta kyauta min kuwa zan aika da tukwici" inji Maamu. Wayar Rumana ce tayi kara ta duba ta ga sunan uncle. Kasa dauka tayi wai kunyar Maamu ai kuwa ta rinka mata dariya wadda tasa ta fita ta tafi dakin Baaba Hure. Tana sa kafa suka hada ido dashi gabanta ya fadi yana zaune shima shigarsa kenan bayan ya kira bata dauka ba. Kamar ta juya sai kuma ta daure ta karasa ta fara gaishe da Baaba sannan ta gaishe shi kanta a kasa. Wani irin dadi taji da ta ganshi kunya ta hanata nunawa. Shi kuwa kallonta yake duk ta chanja ta kara kyau. Baaba ta dan zungure shi. "Nace ba, ai kana da daki a gidan nan ko? To ku tafi can ku gaisa sosai ba a nan ba. Kai ka kura mata ido ita tana satar kallonka kun manta ina dakin. Ni da dakina babu mai korata" Rumana ta tashi zata gudu Baaba tace "baki isa ba yarinya wuce ki bishi kuyi gaisuwar yaushe gamo kada kisa ya kasa komawa bakin aikinsa" ta kare da dariya. Awaisu kansa kunya yaji ya tashi "daga zuwa gaisheki sai ki koreni ko Baaba" Tace "a ranka kana shi min albarka ba...a tafi dai kafin nace tazo ta min tausa" Yasan zata aikata hakan ya fita ta koro masa Rumana wadda kunya ta hanata tashi. "Ina jiranki a daki ki kawo min abincin yunwa nake ji please" yace ya fara tafiya. Sai lokacin ta gane ashe girkin da sukayi nasa ne Allah Yasa tayi kokarin ganin yayi dadi. Da can tana zuwa kai masa abinci ko damunsa da hira dakin amma yanzu kunyar zuwa ma take yi. Dakin su Mama taje duka ta gaishesu sannan ta dauki kwandon abincin ta wuce dakinsa. Zuciyarta na dukan uku uku ta shiga da sallama. Wata katuwar katifa ce a dakin shimfide da bedsheet mai quilt mai kyau. Wardrobe da dressing mirror. A kasan da karfet kalar labulen dakin sai akwatin kayansa a gefe da abin sallah. A gefen katifar yake zaune ta durkusa daga bakin kofa ta gaishe shi. "Yau kuma tsorona kike yi? Gashi kuma kin shigo dakin nan kenan ke da fita sai da safe" Idanu kamar su fado tace "kayi hakuri Uncle" Murmushi yayi "to karaso mu gaisa wasa nake yi miki" Baki ta dan turo "ai mun gaisa tun a dakin Baaba" "Kina son kwana tare dani a dakin nan ne?" "A'a don Allah" Dariya ta bashi duk ta rude. Ba mamaki yasan dole iyaye zasu yi mata nasiha akan meye aure shiyasa take tsoronsa. Ai kuwa bazai bari hakan yayi tasiri a ranta ba. Burinsa yanzu ta koyi sonsa kafin komai. Kamar wadda kwai ya fashewa a ciki ta karasa inda yake. Hannun damansa ya mika mata ta saka nata ciki sukayi musabiha sai dai bai barta ta tafi ba ya janyota ta zauna a kusa dashi. A hankali ya soma magana "rannan naga text ance anyi missing dina amma nazo naga ba haka ba. Maybe daya yarinyar ce ta turo ba naki bane don ke baki taba min text ba" Da sauri ta dago ta kalle shi zuciyarta har tana bugawa da karfi "dayar kuma Uncle?" Ta fada a raunane Farinciki da mamaki ne suka dirar masa. Lallai Rumana ta fara sonsa ko da bata sani ba sannan gashi har da alamun kishi yana gani. Hakan ya kara masa karfin gwiwar ya cigaba da nuna mata soyayya saboda baya son ta tare komai yazo mata wani iri saboda rashin sakewa dashi. "Eh ke naga kamar baki damu dani ba" Da shagwaba tace "nice na turo fa" "Are you sure? Me kika rubuta a naki?" Yadda ta haddace text dinnan ko cikin bacci ta tashi bazai mata wuya ba ta karanta masa yana bin bakinta da kallo. "To kinyi missing dina? " ya tambayeta idanunsa a kanta. Kasa daga kai tayi sai kai da ta gyada a hankali. "I miss you too Umm Ruman. Amma yanzu fara bani abinci" Tana zubawa ta fada masa yau ita tayi girkin yace to bari yaci ya bata maki. Cokalin farko da ya kai bakinsa zafin attaruhu ya kama masa harshe. Da kyar ya iya hadiyewa saboda yadda take kallonsa tana jira yaci yace da dadi. Runtse ido yayi tuwon nan yana sauka a cikinsa yaji ya mamaye ko'ina. Kasa hakuri tayi tana murmushi tace "Uncle da dadi ko? Yanzu ina ta kara koyon girki a wurin Anti" Kallonta yayi yaga murna take tayi masa abinci yace "yayi dadi sosai yau har kyauta zanyi miki" Murmushin da tayi na jindadi har sai da hakoranta suka bayyana. Tace "cinye na kara maka kaga wannan malmalar karama ce" A zuci yace tashin hankali. A daddafe ya kara loma hudu yaji bakinsa kamar ana hura wuta. Da kyar yake iya magana saboda yaji yace mata bari ya nemi yaro cikin kannenta ya siyo masa batir din rediyo. Dakin ta kalla babu wata rediyo a ciki. Shima ya rasa me zaice mata ne ya dan fita don fankar kamar bata masa komai. Tashi yayi yace ta taya shi ci kafin ya dawo su cinye tare. Ko kofa bai rufe ba ta dauki nama ta saka a bakinta. Ihu kawai yaji tayi yayi saurin dawowa harda rufe kofar don kada a ji daga ciki ta tara masa mutane. Ido har ya fara ruwa ta rike baki "Uncle harshena" Kamar yayi dariya yadda ta tashi tana dire kafafu "Me ya sami harshen?" Hawaye yaga ya zubo sai ta bashi tausayi " ya fita daga bakina" Rikota yayi "yana ciki ki nutsu bari na zuba miki juice" Jug din ya dauko kafin ya zuba a cup ta kafa kai a haka amma ko kadan harshenta bai dena radadi ba. "Bai dena ba" tace tana wasu sababbin hawayen "Bude bakin na gani" ya fada a hankali Tana budewa ya soma kissing dinta sai da yaji a ransa duk nacin yajin nan dolensa ya ragu ko bai tafi ba duka ya kyaleta. Kokarin hada ido ya rinka yi da ita kunya tasa ta kasa daga kanta daga kirjinsa "yajin ya tafi ko na kara miki maganin?" Ji yayi ta sake rungume shi tana murmushi don bata san da wane idon zata kuma kallonsa ba "Ya tafi" "Ni nawa bai tafi ba yaya za'ayi kenan?" Dagowa tayi kadan "in baka juice?" "Saboda kirki yayi miki yawa? Wanda naci yama fi naki amma juice din bai korar miki ba sai ni zaki bawa...kuma ma dai nasha ya isheni" "Yaushe?" Lebenta ya rinka zanawa da karamin yatsansa "wanda nasha daga nan ya isa saura ayi min maganin yajin nan ko ki fada min me kike nufi da haka..." yayi mata wannan alamar da hannu "Ko kuma na fadawa Yaya Harisu irin wannan yajin da kika tura min. Zabi daya" ya mata murmushi ita kuwa ta hadiyi yawu da kyar. Babu na zabe duk cikinsu.[15/08, 17:46] ‪+234 803 272 5896‬: *KASHE FITILA*💡43 *Batul Mamman*💖 "Ke nake jira fa" taji ya fada yana murmushi. Dubawa tayi ta ga babu zabin da yayi mata. Idan ya fadi yajin miyar nan yau mai rabata da Anti Ummukulsum sai Allah. Maganin yaji kuwa ko da wasa bata hango kanta tana wannan abin ba...karshen rashin kunya ma kenan! Zabi na uku kuma da wane bakin zata fada masa ma'anar abin da tayi da hannu. Wai waye ma ya aiketa tayi ne? Ya kula da yadda tayi zurfi a tunani a ransa yace yau fa an hada mata da aiki. Hannunta ya riko "Kin bani zabi?" Rufe ido tayi bakin nan an dan turo shi tana magana cikin sauri kuma can ciki a hankali yadda ba'a ji sosai tace "Dakayibakajiyajinyatafiba" "Me kika ce?" Don shi ko kalma daya bai tsinta ba. Sake maimaitawa tayi a hankalin yace bari kawai ya tashi ya fitar da food flask din da aka zuba miyar. Tayi saurin katse shi "Uncle cewa nayi da kayi baka ji yajin ya tafi ba?" Ya daga mata gira daya yana son yin dariya "Da nayi me?" "Abin mana" ta amsa tana kara turo baki. "Wane abu nayi da bashi da suna Umm Ruman?" Ya gane me take nufi amma yana jindadin tsokanarta. Kamar zata yi masa kuka tace "Uncle ka fa gane me nake nufi...ni dai don Allah ka hakura da wannan" Shima irin muryarta yayi "ni dai don Allah bazan hakura ba" Wani siririn hawaye ne ya gani ya fara bin kumatunta sa hannun ya goge shi "dadina da mutum shagwaba. To kiyi kukan idan aka tambayeki a ciki sai kice kiss mijinki ya nema kika kasa. Kuma kinsan ana ganin idonki za'a gane kinyi kuka ayi ta tambayarki sai kin fada. Gara ma ki tashi ki tafi babu ruwana" Dankwalinta ta kwance ta janyo kasansa ta goge fuskarta tana murmushi "kukan wasa ne fa irin wanda mukeyi a makaranta idan bama son bulala" Jinjina kai yayi "gaskiya ban yarda ba wannan wayo ne. Kin gama yiwa malamai fitinar 'yan makaranta kuma nima kiyi min" Dariya tayi "to ba kaine ba..." Nishadin da yake ji a lokacin ya dade rabonsa da irinsa. Komai na Rumana yana burge shi musamman shagwabarta da kuruciya. Addua yayi a ransa Allah Ya bashi ikon kula da komai nata yadda bazata taba kaucewa hanyar da ta sabawa shari'a ba. "To naji kinyi min wayo amma ba hakura zanyi ba. Kawai dai kinci bashin da zaki biya nan kusa. Saura na biyu me wannan yake nufi?" Ya sake hada yatsunsa yadda tayi. Murmushi yaga tanayi harda dan sosa keya. Wannan dabi'ar kuwa yana kyautata zaton a wurinsa ma ta koya domin halinsa ne. Ita dai yau ta shiga tsaka mai wuya daga wannan sai wannan. Dabara zata yi masa kawai don shima ya hakura "A film din 'yan Korea ne fa na gani ko ma'anarsa ban sani ba" Dan fiddo idanu yayi "baki san ma'anarsa ba amma kika yi min. Shikenan kila ma zagina kika yi. Zuwa zanyi na tambayi waye yake kunna miki gashi a kaina ya kare" Gani tayi da gaske ya tashi tsaye bata san lokacin da tace "I love you " Wata irin juyowa yayi a hankali yana kallonta. Ita kuwa kamar ta nutse a kasa. A hankali yace "Me kika ce" "Uncle I love you yake nufi ba zagi bane" idanunta kamar su yo waje don ta tsorata. Bata san yadda kalmomi ukun nan suka tsaya masa a rai ba tamkar wanda bai taba jinsu ba. "Naji ma'anarsu amma da gaske kina yi min son so?" Wannan karon ita ce ta tashi tana neman hanyar guduwa bazata iya jurewa wannan kallon da Uncle Awaisu yake mata ba. Hannunsa ya ware "Give me a hug kafin ki fita please." Tsayawa tayi kanta a kasa tana wasa da hannuwanta. "Kinga komai na tambaya bakya yi ga yaji kin hadani dashi" "To ai kunya nake ji" "Bari nayi miki yadda kika koya min" Ta bayanta ya tsaya ya rungumeta yadda tayi masa wancan lokacin da zai tafi. Da yake ya fita girma da tsaho sai ya rufeta gabadaya ya mata rada mata a kunne "Ke special SS dina ce Umm Ruman. Allah Yayi miki albarka" Amin tace a zuciyarta. A zahiri kuwa tace "Uncle idan na fadi ma'anar SS din zaka taimakeni don Allah" "Toooohhh wane irin taimako kuma. Ko me kike so fada kawai zakiyi" Kwanukan abincin ta nuna masa. "Idan na fita dashi fada za'ayi min kila harda duka ma" "Maganin wannan kawai ki kwana a nan shikenan" Dariyar da taga yana yi ce tasa ta gane tsokanarta yake yi. Ta tabbatar idan Mama ta ga wannan miyar ko bata ji a jikinta ba kunnenta zai bada labari don bayan fada idan ta kama shi ta murde bata da hanyar tsira. "Don Allah kace ya zama assignment irin yadda na baka" Yayi murmushi "Ya zama Umm Ruman, me SS yake nufi?" Sai da tayi kamar mai tunani kada yace tayi saurin canka sannan tace "Son So" Ya girgiza kai "sai hakuri ni Sabuwar Sarauniya nake nufi. Jeki kawai idan kinga zaayi miki fadan ki gudu nan" kan katifar ya koma ya dan kashigida. Hankalin Rumana a take ya tashi. Dama shi take tunanin zai rufa mata asiri gashi ta kula kamar bai damu ba. Awaisu yana kallonta yana dariya. "Jeki mana idan an gama ki dawo ina son magana dake" Mamaki take yi amma kuma tasan dama can idan sunyi laifi baya cikin wanda zaka zo wurinsu ya hana a hukuntaka. Sai dai yayi rarrashi idan anyi hukuncin. Duk wanda ya hana a hukunta to fa sai dai idan ya tabbatar mutum bashi da laifi. Kanta ta dan rangwada gefe muryarta tana dan rawa "na tafi Uncle" Yana danna waya yana dariya ciki-ciki yace "sai kin dawo SS dina" Ta durkusa zata dauki tray din "yau tun safe kunnena na dama ke dan zafi gashi Mama ita kunne take murdewa. Uncle kana da panadol idan ta murde zazzabi ya kamani sai ka bani" Wannan karon da kyar ya iya danne dariyarsa "idan kinje ki bata kunnen hagun tunda shi kalau yake maybe bazaiyi zafin da zaki yi zazzabi ba" Anya kuwa Uncle yana ma sonta ko da ba son so ba ta fada a ranta. Har wani dadi yake ji ga Anti Ummukulsum itama duk wasanta da yara ta iya duka. Hadiyar yawu tayi da kyar ta tuna rankwashin da Antin ta yiwa Iman jiya saboda ta fasa mata plate. Harda sakin ajiyar zuciya ta sake cewa "bye bye Uncle" "See you SS" yace daga inda yake. Tafiya ta rinka yi kamar wadda kwai ya fashe mata. Ko dai kawai tayi tuntuben karya ne kwanukan su zube. Amma kuma masu kyau ne kila ma na baban su Iman Antin ta zuba abincin a ciki. Tana wannan tunanin har Awaisu ya kusa zuwa inda take bata kula ba. Tray din ya karba ya dawo da fuskarta daidai tata. "Kin canka daidai Son So din Uncle Awaisu. Yanzu me kike so ayi da miyar nan kada a taba min mata" Murmushinta kamar gonar auduga tace "zuciyata kamar ta fito don tsoro daurewa kawai nayi" Hancinta ya ja "matsoraciya...jeki ki samo leda sai a juye miyar a ciki. Idan zan fita zan yar don bana fatan kowa yaci kada a kare a gadon asibiti" "Yau ma tsautsayi ne amma next time me dadi zanyi" "Ni kam tsoron girkinki ya shigeni Son So" Dariya ya bata yadda yayi da fuska. Fita tayi ta tafi kitchen ta sami bakar leda har uku ta diba zata fita Mama ta shigo duba nama da take tafasawa. "Ina zaki da ledoji haka kike sauri" Da sauri tace "Uncle ne yace na kai masa" Sanin halinta na rikicewa idan bata da gaskiya yasa Mama tunanin akwai abin da tayi. "Zo nan Rumana" ta dan kaurara murya Haba tuni ta karasa rikicewa "Mama don Allah kiyi hakuri tsautsayi ne." "Me kika yi?" Har ta soma kwalla ta fadawa Mama yajin miyar. Jira take taji ta kama mata kunne sai ji tayi Maman ta sassauta murya alamar tausayawa. "Jeki ki dauko min miyar" Awaisu na jiranta yaga ta shigo a firgice. Flask din miyar ta dauka zata fita yace ina zata kai ta fada masa zata kaiwa Mama ne. Tasowa yayi don yasan halin Mamanta "Muje na bata hakuri don Allah kada ta taba min mata" "A'a Uncle idan dare yayi ma sai tayi fadan gara ma ayi yanzu kawai" Tausayi ta bashi sosai amma kuma duk da yana aurenta yana ganin bai dace ya shiga komai tsakaninta da iyayenta ba kafin ta tare. Hannunta ya riko ya dan matsa "bana son kuka idan anyi miki fada gyara ne kinji ko" "Uhumm" ta iya cewa jiki ba kwari ta fita. Tana kaiwa Mama ta bude ta dandana da cokali "wai Rumana kamar wadda aka aika kama maye" Har ta soma dariya ta gimtse ganin kallon da Mama tayi mata. Kabewa ta ga Mama ta dauko a store dama raba musu akayi har su Anti Ummukulsum din. Ta bawa Rumana ta fere ita kuma ta fita ta nemi yaro ya siyo mata alayyahu. Ga yamma bai samo da wuri ba. Rumana tana kallo Mama ta hada markade na tumatir zalla da albasa nan da nan ta hada ruwan miya bayan ta dafa kabewar. Basu fita ba sai da ta gama nunawa Rumana yadda zata hada miyar taushen wadda ta kusa gama dahuwa da mai yajin sai ga dandanon yayi daidai saboda tasu ta gidan yawa ce kuma bata saka attaruhu ba ko kadan. Rumana ta kalla Mama taji ta kara sonta. "Idan girki ya baci dabara akeyi a gyara ba zubarwa ba. Maza basa son almubazzaranci duk da basu da dabarar kitchen irin tamu. Idan kinyi magriba ki zuba masa wannan miyar ki kai. In koma bazai ci tuwon ba sai kizo a dafa masa wani abincin" "Mama bazaki fadawa Anti ba ko?" Murmushi tayi mata "babu mai ji in sha Allah. Amma idan kika kara nida ke ne. Ki kiyaye cin abubuwa musamman tsami lokacin girki. Idan baki kware ba kina bukatar dandanawa. Kuma dole harshenki zai iya jin dandanon da ya bambanta da na ainihin abinci saboda tsami ko zaki" ***** Sallah taje tayi Mama tasa ta dan shafa hoda sannan ta dauki miya ta fita. Addua Mama tayi mata don yanzu kam ta wuce duka ko murde kunne an zama matar aure. Da taje kofar dakin tayi ta sallama bai amsa ba sai ta murda kofar. Dakin a bude yake amma yana can waje tare da Harisu dawowarsu kenan daga masallaci. Shiga tayi ta ajiye miyar ta dauko wancan plate din zata tafi dashi sai gashi ya dawo. Da murmushi tayi masa sannu da zuwa sannan ta duka gaban flask din. "Mama ta koya min na sake wata miyar da waccan din. In zuba maka?" Kirjinsa ya dafe yana tuna azabar da yasha dazu. Yau naga ta kaina. "Ki bar tuwon kinji my sweet SS. Tea zan sha kawai ya isheni" Bata ji dadi ba ta bude harda tura masa shi kuwa ya matsa yana mai fargabar sake zuba yajin nan a bakinsa don gaskiya bai yarda da girkinta ba. "Wannan tayi dadi sosai kuma na dandana" "Bakinki dinnan bana yarda dashi" Cokali ta dauko ta debi miyar ta saka a baki tana kallonsa "ka gani da gaske wannan babu yaji" "Sai na dandana nima zan yarda" Diba ta sake da cokalin ya rike hannunta ya mayar cikin flask ya janyota tsaye "Bude bakinki na tabbatar kin hadiye" Tana budewa ya saka nasa. Ya kuma yi mata riko mai wuyar kwacewa. Dama abin da yake so kenan. Da ya saketa ne yace "yanzu na yarda babu yaji zuba min yunwa har ta cinyeni" Kasa kallonsa tayi saboda yadda yake mata abubuwan dake sakata jin kunya ta zuba masa abincin ta fita kafin ya ankara. ***** Gimbi sai kai kawo take a daki duniya tayi mata zafi. Ta kira Ovi yafi sau goma ba'a daga ba. A nasu bangaren Rita ta kalli Ovi ganin yadda take murmushin mxugunta. "Sis wai me yake faruwa ne kinki daukar wayar Madam Gimbi" "Kinsan a da naso ne ki auri mijinta saboda mu sami rabonmu a gidan. Amma Boka yace idan akayi auren nan daya daga cikinmu zata rasa ranta. Shiyasa nake ganin gara muci kudinta kawai muyi gaba. Ko maganin da ta karbo last a wurinsa ruwan datti ne kawai nace ya bata " "Ba kya tsoron kada ta gane?" "Zata gane amma sai mun gama da ita. Bani wayar naji me take so. Nasan yanzu haukane kadai batayi ba tunda aiki yake ta baci ga aure yayi" Kafin wayar tayi Gimbi ta dauka rai a bace "Ovi kina kokarin cuta ta nr ko me. Yaya zanyi ta sakin kudi babu biyan bukata" "Kiyi hakuri Madam Boka yace akwai inda aka sami kuskure wurin aikin da kikayi da maganin" Da a gabanta take yadda ranta ke kuna kila sai ta kai mata shaka "sai kace wata sabon shiga zaku ce matsalar amfani da magani aka samu? Sau daya aka samu hakan da Maamu tana asibiti" Ovi jin zata cika mata kunne da fada tace "haba ni nasan akwai inda aka kuskure. To boka yace ko waye silar bata aikin a wannan lokacin sune suke bibiyarki suka hanaki sakat" Gimbi tayi shiru tana son tuna sunan wannan shegiyar likitar da ta hanata shafawa Maamu magani. Kwafa tayi taja tsaki "akwai wata likita da nake zargi don ta saka min ido lokacin. Ki fadawa Boka yayu min maganinta. A rabata da abin da tafi so duk duniya yadda ta taimaka wurin nesantani da mijina. Zan turo miki 200k yanzu ayi komai a gama da wuri. Ita kuma Rumana idan Awaisu ya dawo garin nan da igiyar aurenta Ovi zan baku mamaki. Bani da kirki ke kin sani. Shi kanshi ba don wannan azababben son da na rasa dalilinsa ba da bai isa ya sha daga hannuna ba" Bayan sun gama waya Ovi ta cewa Rita ya zama dole wannan karon a biyawa Gimbi bukata saboda kada ta dena yarda dasu. A cikin daren babu fargaba bare tsoro suka tafi wurin Boka. Kayan tsafinsa ya dauko ya rinka surkulle wanda Ovi da Rita duj yawan zuwansu kullum tsoronsa suke yi. Wata irin kibiya ya soka tun daga kai har tsakiyar wani mutum mutumi ya chake shi a jikin bango. ***** Cikin barci Dr. Yana taji jikinta yana zafi kamar an hura wuta. Lokacin shadayan dare. tayi aiki ta gaji ga girkin da tayiwa Hajiya surukarta bayan ta dawo. Mujahid ta soma kira yana falo bai ji ba. Ido a rufe har lokacin ta ga Gimbi ta biyota da wuka ta soma kuka tana rokonta tayi hakuri. Shure shure take ta yi a kan gadon har ta fado ta bige da bedside drawer amma bata farka ba. Karar faduwar abu Mujahid yaji ya shigo ya ganta a wannan yanayin. Duk yadda zaiyi taki bude ido amma ga hawaye yana ta zubowa. Fita yayi a guje ya kira Hajiya Allah Yasa idonta biyu. Suna zuwa suka ji tana cewa "Gimbi! Gimbi!! Gimbi kada ki kasheni!!!!" Hajiya ta daga kanta ta dora a cinyarta tana kuka don duk irin zamansu ba wai ta tsaneta bane ko don zumunci. "Yana bude idonki waye Gimbi?" Jikinta ne ya saki ta dena motsi sai ga jini ya biyo ta karkashinta yana zuba. Mujahid ya tashi ya fita neman key din mota ita kuma Hajiya tana duba jinin ta dafe kirji. "Innalillahi wa inna ilaihi rajiun...Yana bari kika yi?" Sai a lokacin Dr. Yana ta bude ido da kyar maganarta bata fita sosai saboda zafin ciwo "Hajiya kiyi hakuri niyata sai ya cika wata uku zanyi muku kyakkyawan albishir ashe ba me zama bane" Wani abu ne ya tsaya mata a makwogaro tana tuna yadda cikin mafarki Gimbi kw fada mata sai ta rabata da abin da tafi so. Kuka sosai suke yi ita da Hajiya. Da taimakonta ta tashi ta dan gyara jiki a daren suka tafi asibiti. Sunyi kusan awa biyu sannan aka shawo kan matsalar don jini take zubarwa ba da wasa ba. Hajiya ce take yi mata komai cike da tausayawa tana jira ta sami kwarin jiki ta fada mata wacece ko waye Gimbi. [15/08, 17:46] ‪+234 803 272 5896‬: *KASHE FITILA*💡44 *Batul Mamman*💖 _*Shafa'atu Aminu a madadin dukkanin members na BMN muna yi miki fatan alkhairi da addu'ar Allah Ya karo Son So.*_ Hajiyar Mujahid yadda taga rana haka taga dare wannan asabar din. Tunani ne ya addabeta na son sanin alakar Yana da Gimbi da kuma barin da tayi daidai lokacin da take ambaton wannan sunan. Mujahid din ma a asibitin ya kwana. Bayan sallar asuba da ya shiga dakin Hajiya ta kasa hakuri ta tambayeshi wace ce Gimbi. Dafe goshinsa da yake masa ciwo saboda rashin bacci da fargaba yayi "Hajiya ki bari ta tashi zata yi miki bayani sosai. Ni kaina abin da na sani game da matar kadan ne" Hajiya tace "Allah Ya kaimu ta tashin. Wallahi ko wace ce bata isa ta kashe min jika ta kwana lafiya ba. Idan tana takama da hatsabibanci gidansa tazo. Ni har akwai wanda ya isa ya taba jinina ina raye ban dau mataki ba" Tsoro ne ya bayyana akan fuskar Mujahid "Hajiya tun yaushe kika rufe wannan shafin don Allah akan barin nan kada ki koma abin da ya shude. Tsautsayi ne kawai da kaddara" Tabe baki tayi "sai kuma kayi. Ka kira 'yan uwanka ka sanar dasu tunda gari ya waye su kawo abinci kafin ta tashi". ****** Karfe goma na safe ta wuce Maman Rumana ta shiga kitchen zata dora abincin rana saboda yara da wuri duk me girki take gamawa. Tray din da ta hada na breakfast din Awaisu ta gani nan inda ta barshi ba'a taba ba. Ranta kuwa yayi mugun baci ta rinka kwalawa Rumana kira. Jin bata amsa ba yasa ta zuwa dakin 'yan matan. A kwance ta sameta ta rufa ido a rufe. Kanta tayi ta daka mata duka a baya wanda yasa ta tashi a firgice. Mama ta harareta "Tun daren jiya ban fada miki da safe kije ki dauki abincin Kawunku Awaisu ba? Mutum yazo kin masa horon yunwa tunda bai sami abin arziki da zai iya ci da wuri ba sai bayan magariba. Sannan da safen ma shadaya na neman yi ko karyawa baiyi ba" Idanun Rumanan dama a kumbure suke sai kawai ta soma kuka "Mama bani da lafiya ne" Bata gaskata ba tace "wa kika fadawa a gidan nan?" Tana share ido tace "kafata ce kuma su Hafiza duka basa dakin shiyasa ban fada ba" Jiki a sanyaye Maman ta zauna tana shafa mata baya "sannu bari na dora ruwa sai a gasa kafar kiyi wanka. Allah Ya sauwake." Tana fita ta kira Sajid shima kanin Rumana ne na wurin Anti Amarya ta bashi tray din tace ya kaiwa Awaisu ya fada masa bata da lafiya shiyasa baa kawo da wuri ba. Karo na biyar kenan da yake kiran wayarta bata dauka ya fara tunanin ko abin da yayi mata jiya ne yasa take gudunsa. Murmushi yayi yana tunanin idan ta tare akwai rigima kenan. Sallamar Sajid ce ta katse masa tunanin yana zaune sanye da dogon wando brown da farar shirt. Ko yanayin aiki ne da baya samun isasshen hutu yasa bashi da wani jiki wannan sai Harisu. Gaishe shi Sajid yayi kafin ya tambayeshi ina Rumana ya fada masa bata da lafiya. Hankalinsa ne ya tashi ya matso kusa dashi "me ya sameta? Tana ina?" Sajid ya dan kada kai "ina jin ciwon kafar nan ne ya tashi. Uncle idan tana yi fa bata iya tafiya ranar ko bandaki zata sai an riketa" Awaisu ya yiwa Sajid kallon rashin fahimta. Wane irin ciwo ne wannan yace a ransa. Tare suka fito sai dai kafin ya shiga kofar da zata sada shi da ainihin gidan ya dan tsaya. Kansa ya dan shafa ya fara tunani. Yana mamakin kansa da yadda yake jin nauyin iyayen Rumana yanzu. A da can Mamanta abokiyar shawararsa sannan bashi da na biyun Harisu. Amma yanzu darajar aure baya iya sakin jikinsa akan abu indai ya shafeta musamman da yake a cikin gidansu ne. Ya zama dole ginin da ya soma ya banzatar ya cigaba da yinsa saboda babu yadda za'ayi idan ta tare duk lokacin da zasu zo garin ya tare musu a gida shi ba yaro ba yana rabe-rabe idan zai ga matarsa. Idan ya shiga tabbas akwai yiwuwar haduwa da Mama sannan idan bai je ba sai su iya tunanin bai damu da ita ba. Uwa uba yadda ya matsu ya sanyata a idonsa bazai barshi ba. Shiga cikin gidan kawai yayi ya gaisa da sauran matan gidan da ya gani suna fitowa daga kofar dakinsu Rumana. Har yaje bakin kofar sai kuwa ya jiyo muryar su Baaba da mama. Maamu wadda bai san itama tana ciki ba yaji tana cewa dasu Baaba "Yarinyar nan duk wata haka muke fargaba idan ta kusa a gidan Kawunta. Saboda ciwo dama indai a gida ta fara ranar bata zuwa makaranta. Da yake babu wanda ya damu da lamarinmu lokacin haka zata ci ciwonta na kwana biyu sannan ta ware. Idan munyi sa'a kuma kwana daya take ta tashi " Mama yaji tace "sai dawowarta muka san tana yi amma idan anyi mata allura tana dan samun sauki" "Mata sai hakuri wai kafin ayi maganar ciki da haihuwa ma fa kenan. An fadawa mijinta?" Cewar Baaba. "Ai kuwa a tura yazo maza-maza ya kaita asibiti idan tayi wanka. Sannu kinji Rumanan Maamu" Maamu ta fada tana tashi ita da Baaba. Awaisu na jinsu ya dan ja baya don bazai shiga Mama tana ciki ba. Da suka fito gaishe su yayi ya tambayi mai jikin a ransa yana cewa mai yasa ta zauna a dakin da bazai sake ba. Baaba tace ya shiga tana ciki yayi saurin sake yin baya yana cewa zai dawo ya dubata. Murmushi tayi tace masa yaje dakinta ya jirata tana zuwa zasuyi magana ita kuma ta koma dakin. "Rumana zaki iya tashi?" Mama tace "tun dazu nima nace ta tashi ta kasa kafar taki daukarta" Baaba ta fita ta kira Anti Amarya da kanta tace ta kama Rumana ta mayar da ita dakin ita Baaban saboda a nan hayaniya bazata bari ta huta ba. Suna fita ta mayar da hankalinta ga Mama wadda ta kasa fahimtar dalilin Baaba. "Awaisu na gani a kofar dakin amma nauyi ya hana shi shigowa" tayi murmushi ganin Mama ta dan sunkuyar da kai itama sannan ta cigaba da magana "Dama ina so nayi miki godiya da baki tayarwa mijinki hankali akan auren nan ba. Nasan dole zaki ji babu dadi kiga an hadata da mutum kamar Awaisu mai shekaru kusan arba'in. Amma kamar yadda na riga nasan kin sani kowane bawa yana da kaddarar da Allah Ya rubuta masa" Mama tace haka ne. Baaba ta cigaba da cewa "addua'armu bata wuce Allah Ya basu zaman lafiya da juna. Mu namu auren ma ko shekarunta bamu kai ba. Nasan wacece Rumana a tarbiya shiyasa banji komai ba na bada goyon baya ga bukatar Maamu. Abu na gaba da nake son jan hankalinki shine ko da nan gaba Awaisu ya nemi karin aure saboda yayi alkawarin rabuwa da Gimbi don Allah kada ki tada hankali ganin tana da kuruciya. Bai zo min da zancen ba amma kinsan yau da gobe sai Allah. Ko ba komai ina ganin tayi kankanta da daukar dawainiyar miji da yaransa wanda suka tashi kamar kannenta ita kadai." Mama da taji yar kwalla ta tarar mata saboda tausayin Rumana tace "Baaba kada ki damu in sha Allahu tsakanina da ita sai karfafa gwiwa da fatan alkhairi. Kuma ni a nawa ganin gara yayi aure idan yana da ra'ayi saboda nasan a yanzu kam wani lokacin sai yaji kamar ya zaneta" tayi dariya. Baaba ma dariyar tayi "Yo wannan shirmen nata ai shi ne zai kara sawa ya sota. Ku yaran yanzu baku san komai game da soyayya ba. Misali yanzu da bance ta tafi dakina ba haka zaki barta a nan shi da yazo saboda ita haka zai juya gobe ya tafi. Dan irin wannan lokutan kamata yayi a barsu tare tunda matarsa ce. A haka zasu saba tunda ba wani lokaci sosai tarewa zatayi. Idan akayi tariya tana tsoronsa ko ta kasa masa kallon miji kinga babu kanta." Mama dai kunya taji sosai amma tasan halin Baaba. Ko a gaban waye duk mai girki cikinsu idan Harisu ya dawo ta rinka cewa bata son gulma a tashi a bi miji. Tun suna jin kunya har ya zama indai ya dawo ko tana wurin sai su tashi. ****** Awaisu yana zaune jiran Baaba amma hankalinsa gabadaya yana wurin Rumana da tunanin wane irin ciwo ne yake damunta haka. Muryar Rumana yaji tana cewa bazata iya cigaba da tafiya ba Anti Amarya na cewa tayi hakuri saura kadan. Tasowa yayi ya fito Antin na ganinsa tayi murmushi "wato Baaba turo maka matarka tayi kayi jinya. To ni nayi nan ku karasa" Hannun Rumana ta mika masa ya riketa ita kuwa ta juya tana tsokanarsa. Ko gama tafiya batayi ba Awaisu ya dauki Rumana tana ta mutsu-mutsu ya shige dakin da ita. Kan gado ya kwantar da ita fuskarta da sauran hawayen da take ta yi saboda ciwo. Tausayinta yakeji sosai ya zauna a gefen gadon ya rike hannunta na dama. "Me ya sami Son So dina?" Ga ciwo kafafunta kamar ana sarawa ga kunyar an kawota dakin wurinsa ta rufe ido kawai. Matsawa ya sake yi kusa da ita kamar zai rungumeta kamshin turarensa ya mamaye wurin shi kadai take shaka. "Naji Maamu tace duk wata kike yi. Period pain ne yake kama miki kafa?" Wata irin kunya taji duk da ciwon da take ji ta soma sunne kai. Shi kuwa murmushi yayi yana tsareta da ido gashi yayi kusa da ita sosai "Ashe dai ba kwaila na aura ba. Nana da shekara zaki shaifa mana babyn So" Kunya ta kamata amma dayake ba wuya tayi dariya saboda kalmar kwaila da yace sai gashi tana yi a hankali amma taki kallonsa. Yaji dadi ganin ta dan sake dama tsokanarta yakeyi don ta saki ranta ta dena hawayen. "Kada ki damu kin kusa denawa in sha Allah." Dan ware ido tayi "da gaske Uncle?" Shan kunu yayi "nima sunana Son So kema kuma sunanki kenan" A hankali ta dago ta kalle shi amma bata yarda sun hada ido ba. Wani iri take ji a ranta game da Uncle Awaisu musamman idan yana mata irin wannan abin kamar yaro daidai da ita. "Mace da namiji duk suna daya?" "Mata da miji dai zaki ce" Fuskarta ya gani ta chanja alamun tana jin jiki ya gyara zamansa sannan ya dago kafafunta ya dora a cinyarsa. Janyewa take son yi ya rikesu "Ki bari idan ba kina so muyi rigima ba. Matsa miki zanyi ko zaki ji saukin ciwon." Dogon wandon bacci ne a jikinta rigar kuwa baya iya gani saboda hijab da tasa wanda ya sauko har kusan cinyarta. Tausa ya soma yi mata a hankali yana matsa kafafun tana lumshe idanu. "Tun yaushe kika fara ciwon nan?" Bude ido tayi jin tambayar tasa sai kuma ta sake rufewa. Kamar bata son magana saboda kunyar magana irin wannan dashi tace da ta koma Abuja. "Kenan duk zamanku a can kina wannan ciwon kafar kowane wata?" Kanta ta daga tace eh. Yanayinsa gabadaya ya sauya zuwa takaicin irin zaman da yayi dasu a gidansa. Gimbi ya tuna a matsayin wadda ta zame masa shamaki ga sauke hakkokin da suke kansa yaji ya kara tsanar wannan mummunar dabi'a da ta fadawa a dalilin son zuciya. Muryarsa a hankali cikin nutsuwa take fita yace "Son So bani labarin yadda kike managing a irin wannan lokacin" Ya tabo abin da bata son tunawa ko kadan saboda yana cikin abubuwan da suka saka mata jin haushinsa a lokacin. Ta kwashi kusan minti uku yana kallonta kafin ta fara fada masa yadda suke kwana kuka ita da Maamu domin idan ta gaji da rarrashinta itama kukan take yi. Babu zancen magani sai dai ta gasa mata kafar tunda Allah Yasa kowane daki na gidan akwai heater ta bandaki. Zuciyarsa ta karye sosai da tausayinsu. Da ace zai iya maida hannun agogo baya da ya mayar ya gyara abubuwan da suka gabata. Godiyarsa daya ga Allah daga ita har Maamu duk suna raye da baisan yadda zaiyi ba. A lokacin kuka take yi sosai da ta tuna yadda lokutan al'adarta suka zama lokutan ciwo da kazanta a gareta. "Uncle Awaisu yana so kiyi hakuri da dukkan abubuwan da suka wuce kinji. Sannan mijinki yayi miki alkawarin sauke duk wani hakkinki harda kari. Nasan kinsan komai game da abin da Gimbi tayi min amma duk da haka ba uzuri bane a ganina" Hawayen da yake bin kumatunta yasa yatsansa yana gogewa a hankali. Akan abu da bai kai ya kawo ba Gimbi ta tarwatsa musu farincikin rayuwa. Tsoron kada uwarmiji ta koreta ya kaita ga aikata manya manyan laifuka da sunan soyayya. Cigaba yayi ta matsa mata yana ja mata yatsun karfar daga ita har shi suna jin wani yanayi. Suna haka Hafiza tayi sallama ta shigo da kayan Rumana a hannu. Wai itama 'yan mata harda rufe ido ganin Awaisu yana yiwa Rumanan tausa a kafa. Itama kunyar ce ta kamata tana ta kokarin dauke kafarta sai dai ya rike sosai gashi wani sabon ciwo da yafi na dazu take ji. Dariya kunyar tasu ta bashi yace da Hafiza kayan waye ta kawo "Maamu tace tayi wanka ka kaita asibiti ayi mata allura" Rumana ta kwabe fuska "ni wallahi bana son allurar" Hafiza dai ficewa tayi duk kunya ta isheta tana dariya. Ba jimawa ta dawo da ruwan zafi a bokiti ta shigar dashi bandakin Baaba ta sake fita. Awaisu ya tashi ya miko mata hannu "taso kiyi wanka" "Ni bazani asibitin ba. Allurar kara rike min kafa take yi" Yayi murmushi "naji amma dai ya kamata kiyi wanka kafin na fara toshe hanci matata bata wanka" Daga hijab din tayi batare da ta sani ba ta fara sansana jikinta. Shi kuwa sai dariya. Da taimakonsa ta tashi ta shiga toilet din. Sai da ta rufe kofar yaji tace "Uncle amma zaka fita kafin na gama ko" "Sai kin kirani Son So" ya bata amsa yana daga kayan da Hafiza ta ajiye. Riga da wrapper skirt ne na atamfa sai underwears da bodyspray. Wata leda ya gani ta pad ya tuna labarin da ta bashi dazu. In sha Allah kwalaye zai rinka ajiye mata a gida don kada ta taba nema babu. "Uncle pleaseeeee" "Son So pleaseeee" ya kaikwayeta. Gaskiya bata so ta fito yana nan da ta sani ta kwashe kayanta ta shiga dasu. Kamar mai rada yaji tace "Son So" Shiru yayi ta sake fada yana jindadi sai a na ukun yace mata ya tafi. Ta dade tana gasa kafafunta sannan tayi wanka ta fito kai tsaye daure da tawul. Ganinsa tayi a zaune yana juya bra dinta a hannu yana dagowa suka hada ido yace "wannan ma acuci ce ko size din kenan idan na koma zan hada lefe. Nasan yanzu ance mata komai kari kuke yi" Mantawa tayi da ciwon kafar ta nufeshi gadan-gadan ta mika hannu zata karba saboda kunyar da taji da sauri shi kuma ya daga hannun sama yana kare mata kallo. Kula tayi da abin da yake yi ta kwasa a guje ta koma bandakin tana cewa "Yau naga boni" "Za dai ki ganshi yarinya har me akayi kike gudu tun yanzu" Yadda ya saba jin farinciki idan tana wasu abubuwan haka yaji yanzu musamman idan ya tuna dan jikinta da ya gani. Tashi yayi don kada ta kasa fitowa ya dan jingina da kofar ta waje "Fito ki shirya kinji zan jiraki a dakin Maamu" Sai da ta dan kara lokaci ta leko don ta tabbatar ya tafi. A gaggauce ta shirya saboda kada ya dawo ta koma gadon ta kwanta tana zumbura baki yau gabadaya Uncle ya gama da ita. ***** Hawayen da Dr. Yana take yi sune suka tabbatarwa da Hajiya cewa ta farka. Matsowa tayi kusa da ita ta dafa kanta. "Sannun kinji Yana. Allah zai baki wani. Mutanen Maiduguri na hanya kada su iso kina wannan kukan ki karyawa kanwata zuciya" Yana ta daga hannunta mara kwari ta share ido. Mafarkin da tayi da Gimbi tar take tuna shi kamar yanzu yake faruwa. Mujahid na shigowa ta sake saka wani sabon kukan mai cin rai. Hajiya fita tayi ta barsu yana ta rarrashinta. Bayan kusan rabin awa Hajiya ta koma dauko purse dinta da ta saka goro a ciki taji suna magana. Kara kunne tayi sosai yadda zata ji da kyau. "Shiyasa nace ki dena shiga sabgar mutane a asibitin nan" "Yanzu sai na ga abu da idanu na na dauke kai don bai shafeni ko wani nawa ba?" Ta fada tana kuka Rarrashinta ya koma yi "ba haka nake nufi ba amma kuma ba kowa ne zaki shiga lamarinsa ba haka kawai ya rabu dake. Wannan Gombo din din take ko Gimbo da bakinki kika ce an fada miki tana asiri. Infact da idonki kika ganta..." "Da ban taimaka ba Allah kadai Yasan me tayi niyar yiwa tsohuwar nan. Ban taba nadamar taimakawa mutane ba domin kawar da kai da mukeyi idan abu bai shafemu ba shine babban rashin hadin kan da mukeyi a matsayin musulmi. Ya Mujahid idan har Allah Ya bani iko to duk inda naga rashin gaskiya zanyi kokarin taimakawa." Girgiza kai yayi "ban hanaki ba Yana amma ba kowane abu bane zaki shiga. Wanda yafi karfinki sai ki nemi mutanen da ya dace. Yanzu dubi yadda matar nan tayi mana sanadin zubewar cikin nan. Wallahi bazan yafe mata ba " Yana ta dafa hannunsa "kayi hakuri in sha Allah zamu sami wani amma nima wallahi wannan matar sai na nuna mata kurenta" Hajiya ce ta bude kofar dakin ta shigo tana kallonsu zuciyarta a hasale. "Cikinku waye zaiyi min bayanin Gombo dinnan yadda zan fahimta" Mujahid ya matso kusa da ita ta daga masa hannu. "Wallahi kada ma ka soma cewa nayi hakuri don bazanyi ba. Yana ke nake saurare don wannan mijin naki babu abin da zai iya" Ba don taso ba Yana ta bata labarin da ta samu a wurin Rumana da wanda idonta ya gani. Hajiya ta dan cije lebenta na kasa "Sai tasan ta taba gudan jinin Hajiya Fanta. Hatsabibanci gidansa tazo da kafarta" Yana da Mujahid duka a tsorace suka fara rokonta tayi hakuri kada tayi abinda tayi niyya. Bata sauraresu ba ta dauki jakarta ta fita. Hajiya Fanta mutuniyar Damboa ce a jihar Borno. Tun tana karama take fama da lalurar aljanu wanda da kyar aka rabata dasu. Su suka saka mata fitina, rashin hakuri da zafin nama wurin aiwatar da kowane irin aiki. Bayan tashon lokaci da aka diba ana nema mata magani an samu sun fita sai wata guda daya da ta nace wai bada magani take so Fanta tayi. A hankali ta zama wata karamar yar bori inda daga kallo daya zata iya fadin ciwon dake jikin mutum kuma ta fadi magunguna na gargajiya da zaayi amfani dasu a dace. Har tayi aure ta gama haihuwarta kowa yasanta da sana'arta. Wani babban malami ne su Mujahid da yan uwansa mata suka nema da kyar ya samu Fanta ta amince ta dena bada magani domin lokuta da dama abin yafi kama da wani nau'i na sihiri. Magani da wasu lakani babu wanda bata bayarwa. An rabata da aljanar da kyar amma kafin ta tafi ta nanata cewa duk sanda take neman taimakonta sunanta kawai zata kira tayi alkawarin share mata hawaye. Malamin nan ya nuna mata hanya ce kawai take nema ta dawo saboda haka duk runtsi duk wuya ta kai kukanta ga Allah shi kadai. Labarin Gimbi da abin da tayiwa jikanta da ko numfashi bai fara ba tayi sanadin zubar dashi ya tuna mata da cewa shekarun baya karyar mutum ya kara da ita. Aljanun ma bata shakkarsu balle wata Gimbi. ***** Baaba da kanta taje ta koro Rumana tace suje asibiti. Ba yanzu ake ji ba sai dare yayi ne abin ke tsananta ta kwana tana kuka mai jinyarta ko rintsawa bazai sami yi ba. Mayafi ta yafa fuskarta duk tayi fayau dama haka take yi tana dafa bango ta fito ta shiga motar. Baya ya bude mata yace ta kwanta sosai tace gaba zata zauna amma ya kunna mata AC zafi take ji. Kujerar gaban ya kwantar mata yadda zata fi jindadin zaman ya kaita wani health centre dake kusa dasu. Sunyi sa'a da likita ya rubuta mata allura irin wadda ake yi mata tun dawowarta fika. Jikinta a sanyaye suka bi bayan nurse din da zatayi mata. Allurar ba karamin zafi gareta ba har wani dan tsayawa akeyi ruwanta ya shiga a hankali. Nurse din tana tsartar da ruwan allurar daga sirinji tana dan kada shi Rumana ta zuba mata ido wanda yake cike da kwalla . Awaisu ya kalleta duk ta bashi tausayi yace "kina so na rikeki?" "A'a ka fita" sai ga hawayen ya sauko. Nurse din tayi dariya "bazanyi miki da zafi ba. Hannuna kamar auduga yake wurin allura" Tashi yayi zai fitan don yasan kila kunya take ji ayi mata a gabansa. Allurar ta sake kallo yana daf da fita yaji ta cakumo shi a gigici. "Don Allah Uncle ka rikeni wallahi da zafi allurar" Murmushi yayi "Suna na Uncle?" Ta girgiza kai da sauri "Son So" Nurse din ya kalla shima ba karamin tsanar allura yayi ba don ko ciwo yake aka rubuta allura baya zuwa idan ba yaji jiki ba. "Yanzu dole sai anyi mata?" Wani dadi ya kama Rumana tace "ina fa ba dole bane. Lokacin da ba'ayi min kwana daya nake warkewa" Ya kama hannunta har lokacin nurse din yake kallo "to kinji ki bata magani kawai mu tafi" Rumana sai gyada kai take yi har wani kuzari yana kara shigarta "bari na jira a mota ko Uncle idan ta baka sai mu tafi. Ni kaga bani da lafiya bazanyi ta tsayawa ba" Shi kuwa yace ta tafi nurse din ta kwashe da dariyar yadda suke yi duk su biyun sannan tace idan har Rumana tana son lafiya ta bari ayi mata allurar saboda kada nan gaba kafarta ta sami matsala. Awaisu na jin haka ya janyota yace ta tsaya zai riketa. Haba tuni hankalinta ya tashi ta soma kuka. Rungumeta yayi a hankali ya daga hijab dinta ya kuma janye rigarta kadan. Nurse din na dukawa da allurar zata dan janye zanin kasa ya runtse nasa idon kamar shi za'ayiwa. Kankame shi da Rumana ta sake sosai tana kuka a hankali ya gane an tsira allurar shima ya kuma riketa sosai yana cewa tayi hakuri. Nurse ta gama ta dago kai tana kallonsu. Shi da Rumana sai ka rasa wa akayiwa allurar idan ka kalli fuskokinsu. Kasa hakuri tayi ta tambayeshi yaya suke da Rumana. Bai saketa ba har lokacin tana kuka yace "matata ce Son So dina" "Kun burgeni wallahi. Rumana zaki zama kawata daga yau ko?" Zumbura baki tayi "bayan allurarki da zafi sosai" "Tuba nake amarya bari na danna miki wurin kada ya tashi" Kafin ta kai hannu Awaisu yasa hannunsa a wurin yana dannawa a hankali yana hura daidai kunnenta. Daga shi har Rumana babu mai magana Nurse din ta rike baki kafin ta fita ta rufe kofar tana cewa wannan sai ku makanta mutane ai. Kira taji daga bayanta "Sister A'i maman hudu dagq ina haka?" Daga hannu tayi ta rage murya sosai "hmmm soyayya na gani zata tayar min da tsohon tsumi" Tafawa sukayi suna dariya ganin Awaisu ya fito rike da Rumana tana dingisa kafa. [15/08, 17:46] ‪+234 803 272 5896‬: *KASHE FITILA*💡45 *Batul Mamman*💖 Karkashin wata katuwar bishiyar umbrella fruit dake gaban gidan nasu Awaisu yayi parking din motarsa. Da yake babba ce sai ta yiwa wurin inuwa sosai don suna yawan zaman hira a wurin. Kuma yayi sa'a babu hayaniya sosai saboda yawancin mutane sun tafi cin kasuwar dake kusa dasu mai ci duk asabar. Kallon Rumana yayi tayi bacci sai layin hawaye da yake kwance a kyakkyawar fuskarta. Tunawa yayi da irin kukan da ta rinka yi masa a hanya wai ya bari anyi mata allura. Bata san ko a jikinsa akayi iyakar abinda zaiyi kenan ba saboda yadda shima yaki jinin allurar. Tana kukan yana rarrashi yaji shiru ashe bacci ne ya dauketa. Yanzu da suka dawo yayi parking kallonta kawai yake yi yana kara jin sonta har cikin ransa. Bayan kamar minti goma aka soma kiran sallar azahar. Tunani yake me ya kamata yayi. Da gani tana jindadin baccin musamman da akace jiya kwana tayi tana fama da ciwo. Fita yayi ya zagaya bayan motar tasa hadaddiyar jeep navy blue ya dauko abin sallah. Tagar bangaren da take ya sauke kadan ya zira abin sallar ta ciki sannan ya mayar ya rufe. Sai yayi mata kamar labule babu yadda za'ayi rana ta dameta ko wani ya ganta idan ba gaban motar ya zagayo ba wanda kuma babu hanya don ta kusa taba bango. Sai da ya daidaita mata AC din ya kuma kwantar mata da kujera sannan ya fito yayi sa'ar ganin Sajid zai shiga gida. Kiransa yayi yace ya zauna a bayan motar ya jira shi ya dawo. "Idan na dawo na samu ka tashi yayarka ni da kai ne. Kaga bata da lafiya ka barta tayi bacci" Sajid ya dago kai a dan rikice jin yace zai gamu dashi "Uncle idan ta farka da kanta fa" Hannu Awaisu ya dora a lebensa "shhhh da wannan surutun zaka tasar min ita." "Ita kadai ce taka Uncle mu kuma fa?" Sajid ya fada fuskarsa na nuna rashin jindadi. Murmushi Awaisu yayi yasan halin Sajid da tambaya idan ya biye masa zai iya makara sallah. Robar ribena daya ya dauko cikin wanda ya siyowa Rumana ya bashi ya fita daga motar yana nanata masa ya kula da mukullin da ya bari a jiki saboda AC da bai kashe ba. Har ya dawo daga masallacin bata farka ba sai ma gyara kwanciya da ta kara yi. Gaba ya koma ya zauna ya cewa Sajid ya fita ya tafi gida. Yaro yayi kwal da idanu zaiyi kuka. "Don Allah nima ka barni in sha AC bazanyi surutu ba" Girgiza kai Awaisu yayi yana dariya ya daukowa kansa karfen kafa. Yadda yake da surutu yasan ko hannun Rumana ya taba sai ya kai rahoto cikin gidan. Wayarsa ya dauko kawai yana karanta labarai ba jimawa shima Sajid din ya bingere a bayan motar yana bacci. Sai bayan fiye da rabin awa ya farka ya fita wai zaiyi fitsari. Buga kofar da yayi da karfi ne ya tashi Rumana ta farka ta mike hannu tana mika ta kusa hadawa da fuskar Awaisu. ***** Sajid na shiga tsakar gida ya hau bada labarin Uncle Awaisu yasa shi gadin Rumana yanzu ma tana motarsa tana bacci. Mama kunya ta rufeta ita kuwa Anti Amarya kan Sajid din ta make tana cewa bata son gulma. "Uban surutu idan na kuma ji kana fadin abun da ba'a tambayeka ba sai na dirje maka baki" Dakinsu ya tafi yana hawaye rai a bace an doke. ***** Da sauri Rumana ta tashi tana waige gabadaya kanta ya juye ta kasa gane ina take. Awaisu kuwa hannun da ta miko gaban fuskarsa da tana mika ya damke. "Kwashe min fuska zakiyi Son So?" Rufe ido tayi a kunyace tana cigaba da waige ta gano ina suke "yi hakuri kaina ne ya juye" "Har kinsa na fara jin tausayin kaina" yayi maganar yana son hada ido da ita. Kallonsa tayi ta tambayeshi meyasa yake tausayin kan nasa suka hada ido bata ankara ba. Sassauta murya yayi yana mata murmushi "saboda haka zaki rinka bugeni akan gado idan kina bacci" Zaro idanu tayi "La ilaha illallahu...." "Muhammadur rasulullah SAW" ya karashe mata. "Ni dai babu ruwana wallahi" ta turo baki a rude "Ni kuma da nawa saboda haka kema da naki. Wai me kike zaton ina nufi har kin wani tsorata?" Baki na rawa tace babu komai. Dariya yayi yana cewa tayi ta gama tsoron da firgicewar zata dena ne. Wata irin yunwa taji ta kamata don tun jiya rabonta da abinci. Cikin ta dafe ta kama kofar zata bude taji ta a rufe . "Uncle don Allah zan shiga gida yunwa nake ji" Wani irin kallon yayi mata ta kuma gane dalilinsa taki yin abin da yake so saboda kunya ta sake cewa tana jin yunwa. "Babu inda zaki idan baki gyara sunan da kika kirani ba" A hankali tace "ssssooonnn" don shi dai banda harafin *s* bai iya gane komai ba sai sautin da bakinta ya fitar. Matso da kunnensa yayi daidai bakinta kamshin turarensa ya kara shiga hancinta. "Banji me kika ce ba fa" Dagewa tayi ta saita bakinta a kunnensa da karfi tace " *SON SO* " Da sauri ya daga ya hau dukan kunnen don ji yake kamar ya zama kurma. Rumana ta rinka kyalkyala dariya allurar da aka mata tasa ta manta da ciwon kafa saboda saukin da ta samu. Harara ya sakar mata amma fuskarsa ta fallasa murmushin da yake yi "so kike yi na kurmance zaki kashe min dodon kunne. Zo ki fita kafin ki sa na rasa na ji" Dadi taji yadda yake yi kuma yace ta fita. Bude kofar tayi ta sauka sannan ta juyo tana kallonsa "Uncle na iya maganar kurame fa sai na koya maka" Hannu ya miko kamar zai kamata yace "ki kiyayi zuwa hannuna?" Tayi saurin rufewa ta fara tafiya. Bata yi nisa ba ta sake juyawa "Uncle ka gani" ta fada da dan karfi. Lokacin abin sallar yake cirewa daga window din. Yana dago kansa yaga tayi masa wannan alamar da hannunta na dama fuskarta dauke da murmushi. Bata san yadda yaji dadin hakan ba har kasan zuciyarsa. A hankali yace "Allah Yasa kiyi min Son So tsakani da Allah ba don babu yadda zakiyi da aurena ba Umm Ruman" Yadda tayi da hannun shima yayi mata ta sake jin kunya ta shige gidan a guje. A ransa yace lallai lafiya ta samu. Kafin ya shiga shima drebansa yazo yana bashi hakuri wai ya zagaya ganin gari ne ya manta bai tambayeshi ko zasu fita ba. "Kada ka damu sai anjima zan sake fita amma ni zan tuka kaina. Kai dai ka shiryawa naka tukin na gobe" ***** Wanka ta fara yi sannan ta zauna taci abinci. Tana gamawa kamar jira wani baccin ya sake dauketa. Dama haka take idan anyi allura ta wuni bacci washegari ta tashi garau. Awaisu tare da Harisu suka ci nasu abincin sai ya shiga babban falon gidan ya tura aka kira masa uwargidan Harisu. Tsokakanarsa ta gama sannan ta zauna ya dauko kudade masu yawa ya bata yace gashi nan na hidimar biki. Godiya sosai tayi masa da addu'a ta tashi tace zata kaiwa Harisu. Sai da suka dawo daga sallar la'asar Harisu ya nuna masa ko kadan baiji dadin wannan kudi da ya bayar ba. "Awaisu sai kace wanda ya auri wata bare zaka bada kudin hidimar biki" ya fada rai a bace yana mika masa kudin. "Yanzu Yaya menene a ciki don na bayar. Bani da abin da zan iya biyanka ko na saka maka yawan alkhairan da kayi min" "Ni dai bana so. Addu'ata kawai ku zauna lafiya shikenan" Awaisu yaji dadi kuma yana yiwa kansa kallon wanda yafi kowa sa'ar 'yan uwa. "To don Allah ka bar mata kudin sai su kara a na lefe da zan bawa Anti Baraka" Harisu ya rasa me zaice karshe dai yace "hmmm wannan shine ba mage ba miyau din. Nace bana son na biki kana zancen lefe. To wallahi kada ma ka fara. Idan tazo gidanka ku kare kalau. Amma yanzu kam ko sisinka bana so kuma bazan karba ba" Awaisu ya dage shima "Yaya lefen nan dangi zasuyi ta zuba ido kuma kaga ga dangin uwa" "Shine zaka biye musu ka dorawa kanka nauyi? Kayi gyaran gida ga kayan daki ga wannan zirga-zirga. Babu wani lefe da zaka yi na soke" "Kada muyi haka da kai Yaya" ya dan rage murya. "Mun riga munyi ma. Bari kaji tunda haka kake so a matsayina na mahaifin Rumana nace bazan karbi lefen ba" Dariya maganar ta bawa Awaisu "Yaya harda fidda kokon usuli. To naji amma a matsayina na kaninka dolene na taka rawar gani a bikin Rumana" Wannan karon Harisun ne yake dariya "akwai wata rawar ganin ne bayan sadakinta da ka bayar. Idan ma akwai rawar sai kayi mata idan ta tare" Zuwa yanzu duka su biyun dariya suke yi sosai amma haka suka tashi Harisu ya kafe akan baya bukatar komai. ***** Da sallama Haj Fanta ta shiga zauren Malamin suka gaisa a mutumce. Tarin littattafai ne a gabansa ya sallami yaron da yake wurin suka sake gaisawa da ita. "Ashe Damaturu kika koma wurin Mujahidu, rannan muke maganar da kaninki Maina. Ina fata kowa dai lafiya" Haj Fanta ta dago kai idanunta suna nuni da tsantsar bacin rai "Ina fa lafiya Malam, wata shaidaniyar yarinya ta sako min iyali a gaba. In takaice maka dai haihuwar da nake ta jira daga matar Mujahid ta samu ta zubar da cikin. Ba yadda zanyi ba shiyasa ma ka ganni a garin nan babu shiri" Mal Ridwan ya murmusa sanin hali da rigimar da suka sha da Haj Fanta a baya ya nemi tayi masa bayanin komai a nutse. Duk abin da Yana ta fada mata game da Gimbi ta sanar dashi tare da dan karin gishiri duk don ya amince Gimbi bata kyauta mata ba. "Shine nace wai ko yau daya dai ya halatta na kira Gogojiya ta daukar min fansa." Tana maganar tana kwantar murya saboda bata so yaki yarda. Wani murmushin ya sake yi "Haj Fanta kada fushi ya saka ki yin shirka mana. Har kin manta gwagwarmayar da aka sha shekarun baya? Ko kinsan ba karamin lada kike samu ba da kika hakura da ayyukan da zasu nesanta ki da Allah duk yadda kike jindadinsu. Me akayi akai aljani ke da kika yi imani da Ubangijin aljanun da mutane" Fuskarta tuni ta nuna rashin jindadin kalamansa na farko sai dai maganarsa ta karshe ta daki zuciyarta. "Haka ne Malam ni kaina babu aljanin da zai ban tsoro balle wata karamar alhaki nan. Yanzu meye abin yi. Kada kace na hakura na riga nayi rantsuwa sai na rama. Idan ban dauki mataki ba zuciyata tana iya bugawa cikin dare a rasa me ya kashe tsohuwa" Wannan karon murmushin da yayi sai da hakoransa suka fito. Haj Fanta rigimammiya ce ajin karshe. Ba don karfin addu'a daga iyalinta da imanin da take dashi ba yana kyautata zaton itama da bokar zata zama irin hatsabiban nan. "Babu abin da yake faruwa da bawa batare da sanin Allah ba. Ki tafi gida kiyi kwanciyarki nayi miki alkawari duk wani sihiri da surkullen da matar nan ta taba yi sai ya karye. Addu'a zamuyi babu dare babu rana gani ga almajirai na. Kuma daga naku bangaren kada kuyi sake. Allah Ya azurtasu da samun rabo mai amfani duniya da lahira" Sai yanzu tayi murmushi "Amin, Amin Malam nagode sosai. So nake ayi kaikayi koma kan mashekiya" ta saka dariya. "Ki barwa Allah Shi Yasan ta inda zai kamata. Mu namu addu'a ne kawai." ***** Karo na shida kenan Gimbi tana son kiran Mama taji muryar 'ya'yanta amma ta kasa. Tasan dayan biyu ne zai faru idan ta kira. Ko dai Maman tayi mata fada ko kuma ta rinka mata kallon ta ciki na ciki. Rasa mafita tayi ta jefar da wayar tana jin wani daci a wuyanta. Ta yaya ma za'ayi Awaisu ya kwashe mata yara. Duk da gidan iyayenta ne amma dai yaro sai uwarsa. Ranta har wani suya yake yi bata ga dalilin da zai sa idan kowa ya juya mata baya ba a hada har da yaran da babu wanda yasan wahalar zuwansu duniya da rainonsu sama da ita. Hawaye taji ya sauko mata tasa hannu ta share a fusace. Awaisu da duka danginsa basu isa ta sake musu kuka ba. Sai dai kuma tana gogewa wani na sauka. Haka ta kifa kai akan gadon tana kuka kamar ranta zai fita. Gajiya tayi da kukan ta sake dauko wayar ta kira Ovi. Kamar jira take tace ta samar mata hanyar fita daga gidan zasu jirata a gidan Ovi din tazo suje wurin Boka. Sosai taji dadin shawarar Ovi ta tashi ta dauko mukullin motarta. Dubawa tayi bata da isassun kudi ta bude kit dinta ta dauko daya daga cikin sarkokin da Awaisu ya saya mata tun kafin zuwan Maamu. Sarka ce hai hade da zobe da dankunne da awarwaro biyu. Seti ne mai masifar tsada don a lokacin da ya bata bayan tasha matukar wahalar haihuwar autanta Mu'allim ne har an fidda rai zata tashi. Jefashi tayi a jaka ta shiga kitchen dinta da yake fayau babu kayan arziki sannan ta fita waje tana yiwa maigadi kallon daidai. ***** Rumana ta tashi daga bacci ta sake yin wanka saboda yadda jikinta ke baci sosai a irin wannan yanayin. Gyara jikinta tayi sosai sannan ta amsa kiran Harisu da ya tura a kirawo masa ita. Tana daga labulen kofar falon nasa idanunta suka sauka akan Awaisu. Wata irin faduwar gaba taji da bata taba ji ba game dashi saboda kwarjinin da yayi mata. Zaune yake a kasa ya jingina bayansa da kujera kafarsa daya ya mike dayar kuma ya dan lankwasa ta yana shan fruit salad wanda ya dauko daga dakin Maamu. Harisu ke zaune a kujerar dake kusa da tashi ta shiga ta sami gefen kujerar dake bakin kofa ta zauna a kasa tana gaishesu. Bayan sun gama gaisawa Harisu yace ta dawo kusa da Awaisu ta zauna. Kamar kwai ya fashe mata a ciki haka ta tafi gefensa ta zauna a kunyace. Harisu yayi gyaran murya sannan ya dubeta "Umm Rumana meye matsayina a wurinki?" Kanta a sunkuye tace "mahaifi" "Madalla, shi kuma Awaisu fa?" Tun da ta shigo ta kula ya dauke idonsa daga kanta har taji babu dadi ko tayi masa laifine. Shi kuwa basarwa yake yi kada ya kunyata kansa a gaban suruki. A dan karkace ta kallo Awaisu tayi sa'a suka hada ido sai cewa tayi "Son So..." Allah Yasa irin maganar nan ta ciki tayi ko kadan Harisu bai ji ba shi kuwa Awaisu bowl din fruit salad din ya kusa saki don rudewa zata kunyata shi. Harisu ya sake maimaita tambayarsa ta kuma bude baki har lokacin tana satar kallon Awaisu da dan karfi tace "Son...." Bai san lokacin da ya kai hannu bayanta yana bubbugawa ba da sauri "Ruwa kike *so*, sannu kwarewa kika yi" Dariyar da ya bata ce ta saka ta soma tarin dole harda hawaye. Ga Harisu da baisan me suke yi ba yayi zaton kwarewar gaske ya tashi yana cewa akwai ruwa a cikin dakinsa bari ya dauko mata. Yana shiga Awaisu ya kura mata ido dariyarta tana bashi sha'awa kamar ya dauketa a lokacin "kinci bashi yarinya ki kuka da kanki ranar da zance ki biya" Ita kuwa yadda taga ya rude baya son Babanta yaji wannan sunan ne yake kara bata dariya. Kallon mamaki sosai tayi masa kafin ta fara magana kamar zatayi kuka "yanzu Uncle sai kace sai na biya idan naci bashinka? Kuma ni yaushe na karbi bashi a wurinka" [15/08, 17:46] ‪+234 803 272 5896‬: *KASHE FITILA*💡 46 *Batul Mamman*💖 Bai sami damar bata amsa ba Harisu ya dawo. Cigaba da buga mata bayan yayi ai kuwa ta sake kwashewa da dariya. Da aka bata ruwan kurba daya tayi ta ajiye amma bata yarda ta sake kallon Awaisu ba. Harisu ya sake maimaita tambayar a karo na uku ta sadda kai kasa tace "Uncle ne" "Ya wuce Uncle dinki Rumana. Mijinki ne kuma nasan cewa bakiyi kankantar da zaki kasa fahimtar me ake nufi da wannan kalmar ba" Idonta taji ya ciko da hawaye ta kasa dago kanta don kada su gani. Tana ji ya cigaba da magana tun tana daurewa sai ta soma kuka. "A da kinsan Awaisu a matsayin kawunki ne kawai. Amma yanzu igiyar aure ta shiga tsakaninku saboda haka ina ja miki kunne wallahi Rumana kada ki kuskura raini ya shiga tsakaninku wai don kina matarsa. Aure girma ne dashi da daraja. A yanzu duk duniya babu mai iko dake sama da Awaisu. Kamar yadda na sanar da yayunki biyu da suke gidan aure kema ina horonki da ki rike Allah da ManzonSa iya tsahon rayuwarki. Ke ganau ce ba jiyau ba akan abubuwan da suka faru a gidansa a baya. Da wannan nake baki shawara ki zama zama tauraruwa mai *kunna fitila* a gidan da aka dade da *kashe fitila*. Ki kiyaye dukkan gabobinki daga sabon Allah musamman shirka ita kam kinsan Allah baya yafewa mai yinta idan ya mutu bai tuba ba. Ana ta cewa ke yarinya ce an aurar dake amma ni nasan kuruciya daban zaman gidan miji daban. Kada ki bani kunya kuma kada ki bawa mijinki kunya. Soyayyar da yake yi miki kada ki bari ta zama makaminki na musguna masa. Abu na karshe da zan fada miki kuma gashi a gabana shaida shine ki sawa ranki kinyi aure na mutu ka raba. Duk ranar da taku ta hadaku saboda rayuwar yau da gobe har shaidan ya baki shawarar kiyi yaji to ki sani kiyi kayanki a cikin gidanki. Baki da masauki a gidan nan indai ba ziyara ce ta kawoki ba. Su Haris kannenki ne kuma 'ya'yanki yanzu. Ki rungumesu fiye da yadda kika saba a baya." Kuka take yi sosai tana jin kamar yanzu za'a kaita gidan miji. Harisu ya juya ga Awaisu yana murmushi. "Abu daya zan fada maka dan'uwana. Kai miji ne kuma uba ga Rumana. Ka tafiyar da ita da fuskar da ta dace ku zauna lafiya." Daga nan yace Rumanan ta fita ta jirasu a bakin kofa. Haka ta fita fuska duk hawaye da majina. Hannun Awaisu Harisu ya rike. "Sai kayi hakuri yara biyar ne yanzu a gabanka. Mata duk girmansu basa rabo da shirme da shiririta. Nasan ba sai na fada maka ba amma don Allah ka rike min ita amana" Duka su biyun zukatansu sun karye. Awaisu ya kara karfin rikon da suka yi da hannuwansu na dama. "In sha Allah nayi maka alkawarin bata dukkan kulawar da ta dace. Allah Ya saka muku da mafificin alkhairi. Zanyi kokari naga cewa kamar yadda kake alfahari dani a matsayin kani zakayi a matsayin suruki" Harisu ya kai masa duka a kafada "ana maganar arziki ka sako wasa. Tashi kuje Allah Ya bada zaman lafiya. Na manta ban fada maka ba munyi magana da Alh Saminu yace iyalinsa zasu je Abujan idan an gama biki. Abin Maamu dai baiyi masa dadi ba" "Yaya ya muka iya. Nagode" Yana fitowa ya ganta a durkushe a wurin har lokacin bata dena kuka ba. Hannunta ya kama jikinta a sanyaye suka tafi dakinsa. Kamar kada ta shiga da ta tuna yadda suka kare daga cin tuwo. Sai ta daure don jin nasihar Harisu take tamkar a lokacin yake yinta. Bandaki ya nuna mata shi kuma ya zauna "jeki ki wanke fuskarki magana zamuyi" Allah Yasa ba wani fada shima zaiyi mata ta fada a ranta sannan taje ta wanko ta dawo. A kan kafet ta zauna nesa dashi sai ya rabu da ita. "Umm Ruman" A ladance tace "na'am" "Duk kinji abubuwan da Yaya ya fada ko?" Ta gyada kai. "Don Allah ki zama irin matar nan da ko miji yana so ko baya so sai ta shiga aljanna saboda kyawawan dabi'u da mu'amala" Tana goge hawaye tace "to". "Ranar monday ya kamata ku koma school amma bazaki je ba. Yaya ya nemi Principal dinku za'a karbo miki takardar transfer. Na cike miki form na wata makarantar so nan zaki koma kiyi SSCE dinki" Kanta har lokacin a kasa tace tafi son komawa makarantar da ta baro. "Uhmm uhmm Umm Ruman. Bana son surutu ne a school kawayenki su san kina da aure. Yawancin makarantu basa yarda su dauki matar aure. Inda zan kaiki ma ban fada musu ba kema ko yaya kike da kawa ki bar zancen sai kin gama jarabawa." "To shikenan nagode" ta iya furtawa. Tasowa yayi yazo kusa da ita ya kama hannunta yana murzawa. "Duk kin zama wata saliha ko fadan ya shiga ne da kyau. Amma kada ki manta kinci bashin kirana Son So a gaban Yaya" Dago kai tayi ta soma dariya. "Lallai yarinyar nan baki da tsoro amma nasan ta inda zan kamaki. Sati biyu ne fa ya rage miki ki biya bashi" "Wai da gaske sai na biya. Na zata ko bashin naci kaine zaka biya. Nice fa Uncle, Rumana Son So" ta langabe kai "Abin naki harda blackmail kuma. To Son So na hakura duk abin da ya biyo baya ba biyan bashi bane so ne kawai" Sonta yake ji ko ina a jikinsa yadda take langabewa tana shagwaba. Hancinta ya ja yana son kissing dinta amma baya jin zai hakura a nan gara ya bari sai lokacin da ta dawo gidansa gabadaya. ***** Gaban maigadi Gimbi taje ta zaro wuka daga jakarta jikinsa ya hau bari kamar mazari. "Ko ka bude min ko na yanka kaina kuma nace kaine kayi niyar...." Bai jira ta gama fadin abin da tayi niyya ba ya tashi ya bude gate din a gaggauce. Dariya tayi ta shiga mota tana takaicin yaya akayi wannan tunanin baizo mata ba tuntuni. Da zata fita ya leko yana sauka lafiya ta sha kunu. "Idan ubangidanka ya sami labarin na fita zaka iya rasa aikin nan" "Wa ya aikeni Hajiya. Ke dai Allah Ya kiyaye hanya kawai" Gidan Ovi ta je kai tsaye. Ko shiga batayi ba suka fito ita da Rita suka wuce gidan Boka. Gimbi tana kuka tana fada masa matsalolinta da rashin biyan bukatarsu. Fuskarsa a murtuke yace "Gimbiya kiyi hakuri daga yau babu sauran aiki a tsakaninmu" Yadda gabanta ya yanke ya fadi ko iyayenta ne suka rasu iya tashin hankalin da zata ji kenan. Dan akwatin sarkar ta dauko ta bude ta ajiye a gabansa. "Ka taimakeni ka rufa min asiri ka magance min matsalolina. An raba ni da yarana da mijina ga kishiya. Iyaye sun juya min baya. Bani da kowa sai kai sai su Ovi" Wata rawa ya tashi yayi yana juyi a gabansu sai ga tusa ta fito mai uban karfi hade da wari. Suna toshe hanci sai Rita ta saki tata Ovi ma tayi. Gimbi wari kamar ya shaketa ta rasa dame zata rufe hanci Boka yace "kinga dalilin da yasa bazan kara yi miki komai ba. In takaice miki ma dai babu wani abu da zan sake baki yayi tasiri " Ga wari ga tashin hankali "Boka me nayi haka da zafi?" "Kinsan Gogojiya?" "Abinci ne?" "Aljana ce da ban taba mu'amala da ita ba. Wannan tusar ma ita ta sakani sakamakon aikin karshe da nayi miki. Bansan wa ya turo ta ba amma tayi alkawarin yi min kisan wulakanci idan na sake yi miki aiki kuma tace ki kiyaye haduwarku. Aljanu na kaf sunki zuwa wurin nan saboda ita" Gimbi ta rasa me zata ce. Boka dai ya dage yace ta fita daga ita har su Ovi. Da suka fito su biyun tusa suke kamar su tada jejin Gimbi da gudu ta arce ta barsu. Ji tayi kamar ana binta a guje duk tsigar jikinta ta tashi....Gogojiya tayi wata dariya. Albarkacin musuluncin da ta karba lokacin da Mal Ridwan ya rabata da Fanta yasa bata sabauta Gimbi ba a wurin. Hajiya Fanta bata nemi taimakonta ba saboda shawarar malam amma taji komai kuma babu wanda ya isa ya dagawa Haj Fanta yatsa tana gani ta kyale. Duk yadda Gimbi taso zira mukullin motar tamkar an shafe wurin bata ganin wurin zirawar ta saki mukullin tayi gaba. ga tsoro da gudu tayi titi tana tsayar da motoci da kyar wata tasi ta tsaya ta shiga. Tana ji ana ja mata dankwali da zani irin yadda tasa akayiwa Anti Bebi. Da kyar ta iya karasawa gida ta shiga kamar walkiya maigadi dai bakinsa alaikum. ***** Washegari tun bayan asuba Awaisu ya gama shiri saboda baya son suyi tafiyar dare. Gashi akwai aiki ranar litinin yana bukatar ya dan huta ko yaya kafin wayewar gari. Ruwan tea kawai ya iya sha ya shiga wurin Maamu. Sun dade suna hira duk da sun raba dare jiya. Nasiha take masa akan rikon addini da dena sakaci da addu'a. Daga wurinta yaje ya jima wurin Baaba ya fada mata karshenta bazai sami dawowa ba har a gama bikin. "Babu komai ai dani za'a kawo amarya sai ka gyara dakuna biyu. Wai ina ma take ne miji zaiyi tafiya ana ta baccin asara." Ta fada tana tashi. Awaisu yace "Baaba kyaleta kinsan bata jindadi " "Bari na tura a kirawo min ita kuma bance ka kulata ba tunda kace a kyale mara lafiya" Murmushi yayi ta fita ba jimawa sai ga Rumana ta shigo tana murza idanu bacci bai isheta ba. "Baaba gani" tace tana neman wurin kwanciya akan gadon. Jin ba'a amsa ba tayi kwanciyarta. Sai lokacin ta kula da Awaisu akan kujerar da take gefen kofa. Da sauri ta tashi tana gyara hannun riga. Dogon wando ne da yar riga mai karamin hannu. Kankance ido yayi daga inda yake "Son So haka kike yawo a cikin gida nan da wannan kayan? Bana so please ki rinka saka mayafi ko hijab a kai" Jikinta ne yayi sanyi tana tunanin ko tayi masa laifi ta soma bashi hakuri. Ganin garin da duhu baifi bakwai da rabi ba gashi tasan dai babu kowa sai iya su na gidan. Bakin gadon ya dawo ganin ta damu "ba fushi nayi ba amma ina da kishi bana son kina yawo a haka kowa na ganinki." Goshinta yayi kissing ya tashi zata fito yace ta zauna a dakin ta nemi hijab kuma ya yafe rakiyar kada ya wuce da ita. Daga dakin tayi masa adduar sauka lafiya ta koma tana jin ba dadi. Shi kuwa bata san ganin da yayi mata a haka bane ya ruda shi. Yana mata kallon yarinya ashe ta wuce yadda yake tunani. Ko kadan bazai juri cigaba da ganinta a haka ba shiyasa yayi saurin tafiya. ****** Sun isa Abuja da wuri kamar yadda yaso suna shiga gidan yaga babu motar Gimbi. Maigadi ya tambaya yace tana ciki amma bai san inda mota take ba. Da ya shiga a bakin kofar dakinta ya tsaya tana kwance akan gadonta da kayanta tun na jiya har lokacin batayi wanka ba. "Gimbi ina motarki?" A gigice ta tashi sai lokacin ta tuna inda ta baro motar. Jikinta ne ya hau rawa ta rasa amsar bashi. Ya kula da yadda take yasan bata da gaskiya. "Na baki zuwa gobe ki dawo min da motar nan" kawai yace ya juya ya tafi dakinsa. Gimbi ta shiga tashin hankali. Ovi ta kira ta nuna mata jiya basu ji dadi ba ta tafi ta barsu amma basu ga mota ba. Bayan kuma ko awa daya basuyi da mai saya ba sunyi sa'a duka takardun suna ciki suka yi cinikin gaggawa shi kuma yaji arha banza ya biya ya dauka. Ba karamin tashin hankali suka yi tayi da Awaisu akan motar ba taki fada masa inda take. Kyaleta yayi ya cigaba da shirinsa na zuwan Son So Rumana. A can Fika suma nasu shirin suke yi. Amarya tana ta shan gyara daga wurin iyaye ko ta ina. Ana gobe fara bikin wata 'yar abokin babansu na bayan layi wanda da yayanta yaso Rumanan tazo. Lokacin suna daki da yayyenta mata ana ta chapta da 'ya'yan gwaggwaninta su Baraka sa'aninsu. Da sallama Zee ta shiga tana ta washe baki "Rumana amarya yaya shirye shirye" A darare ta amsa mata saboda ko da can ba wani shiri suke da ita ba. "Dama cewa nayi bari nazo muyi maganar shirin bikin. Naga baki aiko mana da kati ba mu da sauran kawayenmu gashi gobe za'a fara " Sauran fita sukayi sai Iman da Rumana. Rumana tace mata bikin ne yazo a gaggauce ba wani abu zasuyi ba daban da na iyayen. Sake washe bakin nan nata tayi "Hakan ma yayi amma kin ware kawaye masu rakaki Abuja? Kinsan dole aje da kawaye saboda komai yafi tafiya daidai. Idan wata bata rigani ba zanyi miki babbar kawa" Iman ta soma dariya ita kuwa Rumana cewa tayi " Zee baki ji haushi ba ko saboda yayanki?" Zee ta firfito da idanu "akan me idan ba bakinciki ba haushin me zanji. Abuja fa zaki koma zaman aure. Ni dai don Allah aje dani ko abokin mijinki na samu ya ajiyeni a can. Kodayake ance mai kudin kawun nan naku ne. Ni wallahi ko drebansa ne ina so kiyi min hanya kinji" Iman kasa boye dariyarta tayi suka ce indai an yarda a gidansu zasu tafi da ita Abuja. Ledar viva ta hannunta ta nuna musu. "Ai tuni na tambayo a nan ma zan rinka kwana har a gama bikin." Washegari da safe aka fara biki irin na Bolewan Fika. Sunyi taronsu na kwana uku ana gobe za'a kaita aka yi mata lalle mai kyau ja da baki. Tsabar gyaran da ake mata ta chanja gabadaya ta cicciko sai shekin amarci take yi. Ranar asabar da sassafe aka kama hanyar Abuja. Motoci biyar akayi da guda daya ta kaya a haka ma ana ta rage masu zuwa. Tasha kuka dai kamar bazata tafi ba. Maamu tayi ta bata baki tace mata tana nan tafe. Ita da Baaba sunyi rawar gani a wurin bikin nan. Baya gidan suka iso sai Gimbi a daki ta cika tayi fam saboda bakinciki. Guda su Hindatun Bomai da Tikeke suke yi da gayya don taji haushi. Dakunansu duka wani matashi cikin samarin Fika da yake kaiwa shago shine ya nuna musu. Nan aka shiga sauke kaya suna ta hayaniya a cikin gidan. Rumana ta idar da sallah Iman ta miko mata wayarta dake ta ringing. Ta dauka da sallama ganin sunan mai kiran harda faduwar gaba. "Wa alaikum salam wa rahmatullah wa barakatuhu....welcome home Son So. Ina hanya in sha Allah na fita ne saboda bakin su fi saurin sakewa. Ki gaida min su Baaba kafin na iso" Jikinta ne taji yayi sanyi sai kuma tsoro da fargabar yadda zata zauna da Uncle Awaisu a matsayin mijinta. [15/08, 17:46] ‪+234 803 272 5896‬: KASHE FITILA*💡47 *Batul Mamman*💖 *_Jinjinar ban girma ga dan Arewa na usuli_* *_Dan uwan 'yan Fikra Mudan dan asali_* *_Godiyarmu ba adadi don tafi cikin cokali_* Awaisu na ajiye wayar ya mayar da hankalinsa ga abokinsa Nuru wanda yake ta masa dariyar shakiyanci. "Angon Rumana kana burgeni fa. Wani salon soyayya nake gani da ban sanka dashi ba" Awaisu ya shafa sajensa da aka gama gyarawa tare da aski. "Dole ka sami bakin tsokana mana tunda ka baro aikin da ya hanani zaman gida na tarbeta" "Seriously abar maganar wasa wallahi so nake na taimaka wurin kara kafaka a zuciyar Rumana. Kasan na dade ina ce maka yarinyar tana da nutsuwa tun sanda na ganta a gidanka" Tunawa yayi da yadda ta rinka tsokanarsa zuwansa na karshe har tana kiransa Son So a gaban Harisu dariya ta kufce masa a zuciyarsa yace idan ma da nutsuwa akwai fitina. "Yanzu dai a ina zan sami riga irin wadda nake so tunda kaga komai ya kure?" Nuru matarsa ya kira ta kwatanta masa wani babban shagon sayar da kayan mata da yake tashe a Abuja suka dauki hanya shi da Awaisu yana yi masa bayanin cewa abincin tarbar su Baaba gidan Alh Mudi sun dauke masa. Shi har kunya yake ji ma duk da abubuwan da suka faru yasan suna yi ne domin rage girman laifin Gimbi. Kimanin kwana biyar baya kenan da ya bawa Nuru labarin abubuwan da suka faru a gidansa da auren Rumana . Sosai Nuru yaji haushi dama amininsa ne tun Jami'a a Bauchi. Sai dai shi a wani kamfani mai zaman kansa yake aiki. Awaisu bashi da yawan surutu kuma da kunya dai kace uwar 'ya'yanka ke bin bokaye. Shiyasa ya kasa fada da wuri. Nuru ya tausaya masa duk da yace a baya ya dan kula da abokin nasa ya sauya amma baya son zurfafa bincike a rayuwarsa tunda alakarsu bata chanja ba sai in ka cire rashin barinsa ya kawo tasa mahaifiyar su gaisa da Maamu, kullum yayi magana sai ya bashi uzuri har ya hakura. A gaban matar Nurun ya bada labarin itama ta kadu sosai amma dama can ba wata aminta sukeyi da Gimbi ba. Shi kuma yace ya bayar ne saboda itama da surukarta suke zaune ya kare da yi mata 'yan nasihohi akan son zuciya. Washegari sai ga Nuru a bankinsu yace Kubra ta dage sai anyi taro a gidan Awaisu na tarbar amarya. Da fari baiyi tunanin hakan ba amma abokin nasa da matarsa suka dage cewa hakan ba karamin farantawa Rumana da iyayenta zaiyi ba. Dadin dadawa 'yan hotuna da amare keyi da mazansu lokacin biki itama zata samu. Wannan zai taimaka masa wurin kara saka mata nutsuwar zama dashi. Da gaske suka yi ta jan ra'ayinsa sai gashi ana ta shirye shirye sun kama wuri inda za'ayi event din. Abokansu da matansu suka gayyata da gidansu Shuhada da suka dawo daga tafiya sai kuma mutan Fika da basu san za'ayi ba ma. Kusan komai sun gama sai kayan da Rumana zata saka ne Awaisu yake ta ruwan ido gashi har sun iso gari kuma washegari bayan magariba suke son ayi. Kamar yadda Kubra ta kwatanta kofar wani babban shago suka tsaya mai suna *J.J.Maji Palace*. Wurin yaji kaya na gani na fada masu kyau sai tsada. Nan ma dai ruwan ido Awaisu yake yi kowacce ya taba sai yaga tafi dayar kyau. Burinsa Son So ta fito sosai ta kece raini. Yarinyar shagon ya tambaya ko akwai irin wadda amarya zata saka amma fa ba fara ba ta auren nasara. Cewa tayi tana zuwa ta shiga wata kofa sai gata sun fito da wata kosasshiyar mata. Kiba gareta sosai tana tafiya da kyar ta baza zobba a kusan duka yatsunta da awarwaro. Da fara'a ta tarbe su. "Suna na Hajiya Fattu. Ku biyoni akwai wasu rigunan a wannan dakin irin wanda kuke bukata" Suna shiga idon Awaisu ya sauka akan wata doguwar riga golden mai matukar kyau anyi mata ado da yellow din duwatsu marasa turuwa. Doguwa ce da dogon hannu kuma bata cika ado ba amma kana ganinta zaka ji kamar ka dauka. Dariya Fattu tayi don tasan rigar yake so saboda kyaunta. Ganin yadda yake taba jikin rigar a ranta tasan dole ya dauka tuni ta kara dubu goma akan kudinta. Bai musa ba Nuru yana rike masa hannu ya dauko rigar yace yana bukatar mahadi. Fattu ta dauko masa wani mayafi mai wasu irin dutsu mai kyau shime light yellow ta kawo yace saura takalma da jaka. Komai ta hada masa ya bata kati da kanta ta zura a POS ganin manyan costumers ne gashi harda su sarka da abin hannu duka ya saya. "Yallabai naji kuna zancen taro gobe hala mai saka kayan gobe zatayi amfani dasu tunda kun ce na amarya ne?" Nuru yace "ikon Allah ke dai ki cire kudinki mana ki bamu mu tafi" Ta sake dariya "ai naji dadin ciniki ne shine zan fada muku ina kwalliyar amare idan kuna so. Wallahi ba kowa nake yiwa ba ma saboda yanayin aikina." Awaisu ya dan sake kallonta. Lebenta wani irin janbaki ne yayi dau shi ba green ba shi ba shudi ba ga su eye shadow komai ya fito rambajau. Baya fata ko kadan Rumanansa tayi ado irin wannan. Kula tayi da yadda yake kallonta tayi yar dariya "Don't mind me haka nake tawa kwalliyar amma ka bani dama ka ga yadda zan fitar muku da amaryarku" Bai sake magana ba suka fita. Zasu tafi yarinyar shagon ta biyosu tana magiyar kada dama ta wuce su bata taba jin Fattu tayi tayin kwalliya ba duk da kwarewarta. Nacin da ta kafa musu yasa shi amincewa tare da sharadin ana gamawa idan batayi masa ba bazai biya ba. Nuru ya fara ajiyewa a gida sannan ya wuce gidansa zuciyarsa tana dokin haduwa da Son So. ***** Kaf duniya Gimbi gani take babu wanda yake cikin damuwa da bacin rai irin nata. Tasan basu taba zancen daga kanta babu kari ba duk da kishinta amma ko Awaisu zai karo aure ba irin wannan cin fuskar ba. Laifin da yake ikirarin tayi masa har yanzu bata gani ba. Yanzu da bata dauki mataki da wuri ba dama niyar Maamu ya auri Rumana da tuni tasa ya saketa anyi auren. Wane makircin uwarmiji ne bata da labarinsa. Abu daya ta sani tunda bai saketa ba yana sonta har yanzu. Amma ina mafitar dawo da fadarta zuciyarsa ta koma Gimbiyar Awaisu? Anti Bebi ce ta fado mata. Ba don taci amanarta sun rabu ba ai da itace mai bata shawara. Kuma ta tabbatar da sun dade da mantawa da matsalolin nan saboda ita Anti Bebi ko babu boka zata iya zama da makircinta. Tsaki tayi dole itama ta tashi tsaye ta nemi hanyoyin da zata tsorata Rumana ta fita da kafarta ko da asiri ko babu. Guda ta jiyo daga falo hakan ya tabbatar mata da dawowar Awaisu. Mikewa tayi zata fita taji kanta yayi mugun sarawa dole ta zauna zuciya na tafarfasa. Murmushi yake ta yi matan da suke falon suna ta tsokanarsa. Abinci ne kuloli manya uku a wurin suna ta zubawa. Anti Suwaiba tace masa su Baaba suna dakin Maamu. Yana Sallama Rumana na fitowa daga wanka. Dama bandakin ne farko kafin a shiga ciki babu wanda ya gansu. Cak ta tsaya suka hada ido sai ta koma ciki da sauri ta bugo kofar harda hadawa da yatsanta don sauri. Ihu yaji ta saki daga ciki tana washh yace maganin me gudun miji kenan a hankali sannan ya wuce yana murmushi. Kafin ya gaishe da Baaba su Anti Ummukulsum suka yi masa caa ana ta barkwanci. Haj Umma yayar Maman Rumana da matan 'yan uwansu maza sune suke tare masa ana ta dariya. Dadi ya kama Baaba tayi masa sannu da zuwa sannan tace basu gane dakin Rumana ba sannan suna jiransa ya nuna inda zaa jera mata kayan kitchen domin da safe zasu koma. "Haba dai Baaba kamar ana korarku. Akwai walima da za'ayi gobe bayan magriba tafiyarku sai gata ma. Jibi ku huta" Anti Baraka tace "amma dai wasa kake yi ko Awaisu" "Wallahi da gaske nake abokina da matarsa ne suka shirya. Ai dai bazaku tafi muje mu kadai kamar marasa dangi ba" Duk da suna masa kawaicin basa son dadewa a gidan amma ya kula sunji dadi da har yayi wannan tunanin. Tashi yayi da ledojin hannunsa Hindatu tana shigowa lokacin tace suna jira a raba kazar amarcin a aiko musu. Nan fa ta bude kofar sabuwar tsokana ya fita yana dariya. Dakin Gimbi ya wuce tana zaune kamar wata sabon kamu yace yasan tunda suka zo bata fita ba taje ta gaishe da Baaba. "Amma ka rainani Awaisu. Ni Gimbi naje na gaishe da kakar kishiya sai kace wadda aka cewa jeki kya gani" tana magana tana huci Shi kuwa ko a jikinsa yace "to meye maraba, kuma ina so ki kiyaye Rumana ba kishiyarki bace" Zaro ido tayi sosai "to meye matsayinta? Kada kace min nemanta kake yi babu aure da yardar iyayenta" Hannu ya kada yana fita "wannan kuma ya rage naki. Kishiyoyi a sanina miji daya suke aure...." Yafi minti biyar da fita Gimbi tana ta juya maganar Awaisu a ranta. Me yake nufi??? ****** Kafin ya shiga dakinsa ya nuna musu kitchen yace suyi jeren kayan a nan sannan ya bude dakin da ya tanadarwa Rumana wanda duka kayan bukata na dangane da furtuniture da electronics ya zuba. Daga Fika sun taho da bedsheets da 'yan abin da ba'a rasa ba tunda babu iyayen da zasu so aurar da yarsu sikau. Wanka yayi ya kwanta don ya gaji da wuri ya fita. Rumana yake son sake gani amma idanun jama'a yayi yawa kada a ga rashin hakurinsa. Anti Ummukulsum ya kira ya fada mata ya siyowa Rumana riga yana son ta gwada kada gobe a sami matsala. Ya nuna mata baya so kowa ya gani sai goben. "Ko dakinta kuje ta gwada bari na miko miki rigar" "Dakinta da mutane ana gyara zan turo maka ita" Kafin ya sake magana ta katse wayar. Dariya tayi tasan yana son ganin matarsa ne kuma babu dalilin hanawa. Dakin Maamu ta koma ta kirawota. Daga wurin korido suke tsaya tace taje dakin Awaisu yana kiranta zai bata sako. Gabanta taji yayi wani irin bugu ta kasa ko da daga kafa balle ta tafi. Anti Ummukulsum ta zare mata ido tace ta wuce kafin ranta ya baci. Yatsanta data matse a kofa ta dagowa Antin idonta cike da hawayen tsoro tace "ciwona ne yake zafi Anti bazan iya zuwa ba" Haba ta rike tana kallonta "Rumana ke da ba da yatsun hannu kike tafiya ba meye zai hanaki zuwa. Daure kije sai kice nace ya baki magani " To kawai tace ta nufi dakin nasa rike da hannun da ta manta yana zafi sai yanzu. Anti Ummukulsum ta girgiza kai tana tausaya mata. Tunda suka iso ta kula jikinta yayi sanyi. Zama a matsayin matar Awaisu kadai ya isheta to ga Gimbi kuma a gidan abin yayi mata yawa. Da kukan tayi sallama ta shiga dakin bayan ya amsa. A bakin kofa ya tarota jin tana kuka. "Waye ya taba min Son So uhmm? " Yatsun da ta matse guda biyu ta daga tana nuna masa. So take kawai yace ta fita don ji take kamar ko numfashi tayi a dakin idan ta fita za'a gane. Karo na farko da ta taba shiga dakinsa kenan duk zamanta a gidan. Ba don a tsorace take ba da tace dakin ya hadu kamar mai shi. Hannun nata ya kalla "me ya same shi?" "Anti tace nazo zaka bani magani. Matsewa nayi da kofa" Idanunta sun cika da hawaye yasan tsoro ne ya cikata yace akwai aiki a gabansa. Yatsun ya kama sai kawai ta fashe masa da kuka. Yanzu duk wanda ya ganta cewa za'ayi daga dakinsa ta fito ko da tace Anti ce ta turata karbar magani. Hanyar gadonsa ya ja hannunta ta soma turjewa jiki na rawa. Kin sakinta yayi sai ga hawaye kamar an bude famfo. Cikin kuka tace "Ayya Uncle ni kam naga boni yau din nan" Dariya yaso yi sai ya matse yace "ina yake" yana zaunar da ita akan gadon. Kallon rashin fahimta tayi masa yace "kince kinga boni ni kuwa ban ganshi ba" Kanta ta nuna "ba gashi ba.ni.anan dakin.da.....daa...kai!" Daga mata gira yayi yana tsaye a gabanta "amma kina da matsala, ke da kika zo karbar magani. Dauko miki zanyi kisha saboda kada kiyi zazzabi" Yana kallo duka hannuwanta biyu tasa ta dafe kirjinta irin na hankali ya kwanta ta dago kai harda murmushi "ashe magani nazo karba fa. Bani sai na sha a wurin Baaba" ta mike tsaye sai ya sake komawa gabanta ya tsaya. "Ki dena murna nan din dai zaki dawo ki kwanta. Yarinya sai tsoron tsiya duk kin firgice" yantsun nata biyu ya riko har ta danyi kara sai ta ga ya saka a bakinsa. Kunya irin wadda bazata misaltu ba ta kamata tayi kasa da kanta jin yadda ya mata a yatsun. Rungumeta yayi yana jin harbawar zuciyarta da gudu. Sun dauki lokaci a haka sannan ya cire yatsun daga bakinsa ya dago kanta suka hada ido tayi saurin rufe nata. "Ga maganin nan, idan kinji ciwon ya dawo kizo na sake baki" Yana kallon bakinta ta dan turo shi ido a rufe tace "shiyasa nace maka naga boni don Allah ka barni na tafi kada a nemeni" "Zaki ganshi dai amma ba yau ba. Kuma babu me nemanki duk 'yan rakiyar nan wurina suka kawoki" Bakinta yayi ta bi da ido sai kuma ya dauke kansa shi kadai yana ayyana abubuwa. "Ga kaya can ki gwada na gobe ne" Ido daya ta fara budewa don bata son hada ido dashi. Ganin ba ita yake kallo ba ta bude dayan tana kallon inda ya nuna. Gaban ledojin taje ta durkusa tana budewa. Kayan sun tsorata ta saboda kyaunsu ta dago rigar tana dariya "Uncle" tace ya bata rai tayi saurin gyarawa "To Uncle Son So kayan mene ne?" Komai na Rumana yana burge shi. Sai ya tuna da Nuru yace masa wannan soyayyar kila hadda hakkin rikonta da ya kasa yi a baya Allah Ya jarabce shi da son ta. Hamdala yayi a zuciyarsa shi kam ya dace . "Akwai walima gobe da na shirya to welcome you Son So" Tashi tsaye tayi harda tsalle "da gaske? Kuma wannan kayan zan saka? Unc....Son So nagode. Bari naje na gwada" Hanyar fita tayi ya janyota ta fado jikinsa suka zube akan wata resting chair doguwa a dakin. "Not so fast Son So, a nan dakin zaki gwada. Kina so kowa yaga kayan ne kafin gobe?" Yanayin da suke ne ya sa ta shiga tashin hankali ya fada a kwance tana kansa ga ledojin hannunta sun zagayesu. da taimakonsa ta tashi yace tayi sauri ta gwada tunda kiyastawa kawai yayi girman. Takalmi dai yasan size dinta rigar ce baya son a sami matsala. Tasan bazai bari ta fita da ita ba sai ta nufi toilet. Tana murda handle din yace yanzu yayi wanka ya jika ko'ina. Jinsa kawai take yi bata yarda ba. "Ki saka a nan kada ki jika musu idan batayi ba zan mayar ne" Hawaye ya sake gani ya girgiza kai. Su amare wato kuka baya yi musu wahala. Ango na murna suna kuka. Da taushin murya yace "Ba kya so na kalleki?" Bata iya amsawa ba sai gyada kai. "To bazan kalla ba yi sauri ki gwada" Wurin wani working table da kujerarsa yaje ya zauna inda ya ajiye laptop da takardu. Da sauri ta cire rigarta tana yi idonta kyam a kansa kada ya juyo ta saka gown din. Laushin rigar kadai ya isheta jindadi bata san sanda ta fara juyi ba kasan rigar yana budewa ta soma dariya da tafi. Dogon takalmin mai madauri ta saka ta tashi sai ji tayi kamar zata fadi. Anya zata iya tafiya dashi kuwa ta tambayi kanta. sai dai fa komai na kayan ya burgeta sosai ta sake yin juyi taji ta tafi luuu zata fadi. Awaisu da yake ta kallonta ta screen din laptop dinsa batare da ta sani ba ya taso da sauri ya rikota. Ajiyar zuciya tayi tana kallon yadda komai yayi mata daidai a jikinta. Shima kallon nata yake yi tun yanzu ba karamin kyau tayi ba. "Kinyi kyau Son So" Tayi wata dariyar jindadi "thank you" "Idan takalmin zai baki wahala sai na siyo miki wani da wuri" "A'a don Allah ina son wannan din. Ina naji zan fadi sai na rike Iman" "Zaki sa na cewa dreban da ya kawosu ya mayar da ita Fika yanzu. Idan zaki fadi mijinki ne support dinki kinji ko" "Naji Uncle Son So...nagode" ****** Washegari da wuri suka sake tashi aka karasa duk wani gyara da za'ayiwa dakin Rumana da kitchen. Hatta kayan sawarta wanda suke cikin akwatuna uku manya manya da Harisu yayi mata duk an jere a drawer Anti Baraka ta kwashe mukullan. Rumana da Iman da sauran 'yan uwansu daki daya suka kwana cikin na baki. Yayyenta mata biyu suma duka tare suke sai Zee da take ta jiran ganin ma'aikatan gidan maza don ta mika kokon bararta. Ita dai ta sami mai aiki a Abuja kowane iri ne yadda a Fika ana cewa a ina take aure za'a ce a Abuja. Nacin da ta kafa musu yasa Mama da kanta tace a taho da ita. Tun karfe biyar Hajiya Fattu ta iso gidan. Dakin Maamu aka kaita ta gaishe da Baaba sannan ta nemi ganin amarya. Rumana na shigowa Fattu ta tashi ta tarbota tana kare mata kallo " _perfect_, gaskiya angonki ya iya zabe. Yanzu wanka zaki fara yi kafin mu soma kwalliya" Baaba ta dafe kirji tana kallon fuskar Fattu da irin kayan jikinta. Sarka har ciki ga su awarwaro ko yaya ta motsa sai kaji kachauu. "Kece mai mata kwalliyar?" Baaba ta tambaya. Hajiya Fattu ta wani murmushin burgewa "angonta ma bazai ganeta ba idan na gama" Baaba tace "kwarai kuwa, Allah Yasa kada yayi tunanin gamo yayi. Bari na baku wuri....Rumana sai ince yau kinga boni da kike yawan kira ra'ayil aini" Sai da kowa ya fita Fattu ta bata wani mulmulen abu a leda ashe sabulu ne tace tayi wanka dashi. Rumana ta shiga tana saka masa ruwa kamshinsa mai matukar dadi ya gauraye bandakin. Ta jima a ciki tana wanka sannan ta dauro alwala ta fito. Man da zata shafa ma ita ta bata. Nasa kamshin ya ninka na sabulun. Dadi ya kamata ta saki jikinta da Fattu. Wasu turaruka masu maiko ta sake bata ita dai komai akace tayi tana yi. Jikinta tuni ya koma wani sulbi da kamshi sannan Hajiya Fattu ta soma nata aikin. Zee aka bari gadin kofa sai da aka kira magariba Iman ta chanjeta lokacin sun gama shiryawa itama taje ta shirya. Anti Baraka ce tace kowa ya fita Awaisu yace a kaisu wurin taron. Ya gama nasa shirin cikin wata suit mai bala'in kyau coffee brown sai shirt din light brown da tie shima coffee mai farin stripes Sai takalmi da agogo duka kalar shirt din. Kallon kansa yayi a madubi yayi dariya wai bikinsa ne da Rumana. Da ya fito ko'ina tsit duk an tafi dama yace kada su jira zai taho da Rumana. Gimbi ya gani ta fito tana leka falo saboda shirun da taji. Ganin yadda yayi mata kyau sosai yasa ta tsaya kallonsa tana tuhumar kanta me tayi ya rabata da masoyinta. "Dama yanzu zan fada miki zamu je wurin walima kada kiji gidan shiru" Harararsa tayi "sai yanzu zaka fada min?" "Kinga laifina? Naji tsoron sanar dake da wuri kada ki kira bokayenki ku shiga ku fita taron yaki dadi. Sai mun dawo." Wuce ta yayi sai dai a ransa yana jin wani iri. Tausayi Gimbi take bashi ba na komai ba kuwa sai na yadda taki saduda ta dawo daga rakiyar shaidan...idan mutuwa ta risketa a wannan yanayin shikenan tazo duniya a banza. Mata da yawa suna aikata shirka da sunan soyayya amma idan zasu duba zukatansu sosai sun san cewa son zuciya ne kawai yake dibarsu. Kofar dakin Maamu aka bude Hajiya fattu ta fito tana masa dariya "ango na cika aikina. Yadda yarinyar nan ta shiga raina na yafe kudin" Gabansa ne ya dan fadi ganin irin nata adon ya fara nadamar daukota. Matsawa tayi gefe Rumana ta tako a hankali yana binta da ido har ta iso gabansa ta tsaya. Ganin ya kasa motsi bare magana sai tasa tattausan hannunta ta riko shi harda lankwashe yatsun cikin nasa. Magana take yi a nutse tana lumshe ido "Uncle Son So" Tun daga kanta har kafa yake kallo "na'am Son So" Fari tayi da ido "nayi kyau?" "Mun fasa zuwa wurin muje dakina na sake ganin kwalliyar sai na fada miki ko kinyi kyau" Juyawa tayi wurin da Fattu take sai dai tuni tayi falo ganin yadda Awaisu ya rude da yaga Rumana. Ita kuwa ta kyabe fuska "Hajiya Fattun nan ce fa tace inyi maka haka idan mun fito zaka ji dadi. Daurewa nayi sosai kuma gashi ta janyo kace an fasa zuwa" Hannuwansa yasa a kugunta yana sake kallonta. Wani irin rolling Fattu tayi mata bayan ta daura mata wani dankwalin ta ciki kalar rigar saboda kada maikon gashinta ya bata mayafin. Fuskarta sai ta fito sosai. Ga wani kamshi yana fizgarsa ko ta ina. Ba don ana jiransu ba sai ya bata kwalliyar nan a sake wata. Da kyar ya saita kansa suka fito falo yayiwa Fattu godiya yace kuma idan babu damuwa gaskiya zai turo mata Rumana ta koya mata kwalliya. Dariya tayi tace tana jira sai sun zo. Kusan tare suka shiga mota ta fara fita suka bi bayanta. Awaisu tuki yake kawai hankalinsa yana kan Rumana. Ita kuma kunyarsa saboda kallon da yake yi mata yasa ta kasa sakewa. Motoci suka gani a wajen da yawa har yana tunanin anya duka masu amsa gayyatarsu ne kuwa? Wani matashi ne yayi saurin komawa ciki ya sanar da isowar amarya da ango. Wata waka suka ji tana tasowa daga ciki ana ambaton sunayensu ana wasa amarya Rumana da angonta Awaisu. Kafafunta taji sun soma rawa kamar bazasu dauketa ba Awaisu ya rike mata hannu a hankali yace "yau taki ce Son So kada kiji tsoro ranar farinciki ce" Sake damke hannunsa yaji tayi suka soma tafiya a hankali Mudan Dan Arewa yana wakesu don gabansu ya dawo yana wakar suna tafiya har suka je mazauninsu suka zauna aka hau tafi. Maman Gimbi bata je ba amma ita da alhaji Mudi sun fadawa yaran babansu ya auri Rumana yanzu itama mamansu ce. Nasiha tayi musu yadda kwakwalwarsu zata dauka banda rashin kunya ko raini tsakaninsu sannan ta saka musu kayan da Awaisun ya kai yace su yake so su saka yau. A wurin su Baaba suka zauna sai da suka ga zaman su Awaisu suka tashi duka su hudun suka tafi wurinsu. Mazan na jikin babansu Daula ta rungume Rumana tana cewa tayi kyau akayi musu hoto a haka. Shuhada ma tazo kwanansu biyu da dawowa daga Singapore. Har wurinsu taje suka yi hoto tace da Rumana sai ta kawo mata ziyara gida. Yadda taga Awaisu bai iya boye soyayyarsa ga Rumana ya tuna mata da T dinta ta sake dankawara Anti Bebi Allah Ya isa. Taro yayi kyau sosai anci an sha kowa ya tafi cikin farinciki. Duk da ba'a tashi daga taron da wuri ba amma washegari kafin shabiyu mutan Fika sun kama hanya bayan doguwar nasihar da aka sake yiwa Rumana. Kuka take yi sosai idanunta sunyi ja kamar an zuba barkono. Sai da motar karshe ta tashi ta koma ciki ta bar Awaisu da maigadi suna magana. Hanyar dakinta da ta fara shiga yau da safe Baaba tayi mata fada shi ta nufa. Tana tafiya taji an damko wuyan rigarta an shake. Da sauri tayo baya ta juyo Gimbi ta gani gabanta ya fadi. "Yau na tabbatar danginku kwadayayyu ne sannan kuruciya tana cinki shiyasa kika amince kika dawo gidan nan. Tun motarsu batayi nisa ba kice su dawo su daukeki kafin jikinki ya gaya miki. Abban Haris bazai taba zama dake ba. Yarinya baki fi cikin cokali ba na tsaya ina magana dake saboda wulakanci. Ki bani numbar uwarki da bata san ciwon haihuwarki ba inyi da ita" Rumana taji haushi kamar tayi kuka ta daure ta tattaro duk wata dakiya da take da ita ta yiwa Gimbi wani kallo shekeke "Anti kenan ni din dai cikin cokalin da na sace zuciyar Son So nice daidai dake." Zuciyarta har tsalle take yi kada Gimbi ta kai mata duka tayi saurin fara tafiya sai kuma ta tsaya "Anti dama ina son muyi maganar rabon kwana. Idan Son So dina ya kiramu nasihar kishiyoyi ni dai kwana uku-uku zan ce ina so saboda gaskiya biyun nan da aka saba yayi min kadan. Ukun ma dai maneji zanyi kada na shiga hakkinki." Kafin ta amsa da sassarfa ta bar wurin kada ta saki fitsarin da ya kamata na tsoro. Tamkar an kafe Gimbi da guduma haka taji. Wai ita Rumana take yiwa zancen rabon kwana. Tashin hankali da ba'a saka masa rana. Gumi ne ya rinka tsatstsafo mata ta rasa me zata yiwa yarinyar nan ta huce. Tafi taji daga bayanta ta juya taga Awaisu yana dariya. Ashe duk abin da sukayi akan idonsa ne. Shi ya taho da sauri ya rarrashi Rumana ne ya samesu a wannan yanayin. A harzuke tace "Ka jawa yarinyar nan kunne wallahi bazan dauki raini ba." "Tsuntsun da yaja ruwa.."ya fada ya yana wuceta. Tsoro ne ya kamata kada zuciyarta ta fashe saboda bakin ciki sai ta koma dakinta kawai. Rumana najin an murda kofar dakinta hantar cikinta ta kada tsoro ya cikata tana tunanin Gimbi ce. Ganin Awaisu ta tashi da gudu taje ta rungume shi tana ajiyar zuciya. "Yaya akayi Son So?" Har lokacin jikinta na bari tana jin kamar Gimbi zata zo ta sameta nan "Uncle kasan me nayi kuwa? Taba zuciyata kaji ina jin jinina ne ya hau" Dariya sosai ta bawa Awaisu yana rungume da ita ya dagata yana tafiya hanyar gadonta "ba rabon kwana kike so ayi ba Son So, nima kwana biyun gaskiya sunyi min kadan" Kokarin sauka daga hannunsa tayi jin abinda yace. Wannan karon banda tsoro harda kunya. Jikinta sanyi kalau lokacin da ya kwantar da ita akan gadon. "kaji abinda nace?" Yayi murmushi yana zama a kusa da ita. Tashi tayi zaune "to wallahi wasa nake yi kuma...kuma ma...kuma ni ban san meye rrrabbbon kwanan ba" Janyota yayi tana ta zillewa "ki nutsu ma'anar rabon kwanan zan fada miki"*KASHE FITILA*💡48 *Batul Mamman*💖 *_Kin cancanci fiye da haka Aisha Maman4H....Gaisuwa tare da fatan alkhairi._* Faduwar gaban Rumana ta tsananta ganin yadda Uncle Awaisu ya riketa ga abinda bata taba tsammanin faruwarsa ba wato hada wurin kwanciya dashi. Shiyasa gabadaya ta rikice har take ganin gara ace a gaban Gimbi take a tsaye tana jiran ta kai mata duka da wannan katuwar kunyar da ta lullubeta. Idanunta ta runtse sosai tana fitar da numfashi da sauri shi kuwa ya danneta da rabin jikinsa saboda ta dena kokarin tashi yana kallon fuskarta. Murmushi yayi ya ja hancinta da yatsu biyu "Wai waye ya firgita min amarya ne na kula tun safe yau wani tsorona ma kike ji" Shiru tayi kirjinta yana dukan uku uku saboda numfashinsa da take ji ya kara yin kusa da fuskarta. "Kinga ni kawo kunnenki yadda na fada miki wacece kwaila zan fada miki meye rabon kwanan da kike so ayi kwana uku na maneji" Jin yayi saitin kunnenta ta dago hannu a tsorace ta dora akan bakinsa saboda ko kadan bata shirya jin me zai fada ba. Har yanzu bata manta kunyar da ya bata ba da ya fassara mata kwaila a Fika. Cikin sarkewar harshe tace "na tuna ashe ma na sani ba sai ka fada ba" Lumshe ido yayi yana shakar kamshin tafin hannunta mai laushi akan bakinsa ta kula da yadda yake yi ta zame hannunta a hankali zata tashi ya kara sakin jiki ta danyi kara cikin sanyin murya mai dadi tace. "Wayyo Son So zan karye fa" Har kasan zuciyarsa maganar ta shige shi ya rinka jin sonta yana kara fizgarsa ya rungumeta sosai a jikinsa yana mamakin wannan so da yake mata. Ita kuwa kara tsorata tayi ta rasa yadda zatayi tasa ya tashi kawai sai tace masa tana jin yunwa. Tashi yayi zaune ya dagota a jikinsa. "Me kike son ci?" "Su Anti sun ce akwai komai na girki a fridge da store bari naje na dafa mana" tana magana tana sauke kafafunta daga kan gadon. Wata irin janyowa Awaisu yayi mata ta fado cinyarsa ya kalleta fuskarsa kamar zaiyi mata kuka yace "ki rufa min asiri Son So har yau bakina bai manta yajin nan da kika gasa shi dashi ba" Dariya sosai Rumana ta rinka yi harda rike ciki shi kuwa yana binta da kallo cike da jindadi. Idonta harda hawaye don mugunta ta dan bata rai "kowace amarya mijinta yana son cin abincinta amma ni tsoron nawa ma kake yi. Nasan ma cewa zakayi ban iya girki ba" Hawayen dariyarta da ta mayar kamar tana kuka ya hargitsa masa lissafi ita kuwa tana ta dariya a ranta. "Waye yace miki amare suna girki? Daga gidan su miji ake kawo fa. Tunda mu munyi nisa na yarda zan siyo miki har ki gama kwana bakwai dinki a fara rabon kwana" ya kashe mata ido yana murmushi. Sake bata rai tayi bakin nan ta turo shi gaba tana wasa da yatsun hannunta kamar da gaske bata ji dadi ba "Iman jiya ta koya min wani girki tace yana dadi aci as breakfast. Ko yi banyi ba kana cewa zaka siyo bayan na iya" Ajiyar zuciya yayi shi dai gaskiya baya marmarin sake cin abincin Rumana nan kusa sai ya tabbatar da iyawarta. "Fada min naji irin abin da ta koya miki din sai na rakaki kitchen din ma muyi tare" "Yeeeyyhh" ta tashi daga cinyarsa dama a dofane take ta danyi tsalle tana dariya. "Sunansa Indomie mai romon dadi" Awaisu ya koma yayi kwanciyarsa yana tunanin sawa ta hakura don dole. Ko ta iya girki yafi son su yini tare ba wai ta tafi kitchen ta barshi ba. "Kiyi hakuri Son So ni ba mai son Indomie bane dama." "Wannan fa mai dadi ce...nama ake yankawa kanana sosai amma da yawa sai yayi laushi a jajjaga attaruhu da albasa...... " Zama yayi ba shiri jin ta ambaci attaruhu "ina jinki Iman din nan da gani ta koyi mugunta a zaman boarding da tayi. To kuma attaruhun nawa ake sawa? " Ba karamin dakewa tayi kada ta fashe da dariya ba saboda yadda yayi da fuska. Da yatsun hannunta take masa lissafi "tace idan guda daya ce karama attaruhu biyu da rabi sai rabin albasa. Idan biyu ce kuma attaruhu biyar cif da albasa madaidaiciya daya. Soyawa ake fara yi sai a hada a ruwan naman a saka indomie din. Amma tace idan superpack ce guda hudu ake sawa a daya" Daga labarin kawai yaji kamar dakin ya fara daukar zafin yaji ya taso gabanta ya tsaya. Kasa cigaba tayi saboda yadda yayi mata kwarjini sai ta ganta ta koma yar karama a gabansa. Kafadunta ya dafa tare da daidaita fuskarta da tasa "Zanyi komai domin faranta miki Son So amma wannan romon azabar ba dani ba...naga alama a gadon asibiti kike so muyi amarcin nan" Tun kafin ya daga kansa Rumana ta soma dariya harda kyakyatawa. Sosai taji dadin yadda ta ruda Uncle Awaisu ya mika hannu zai kamata ta zille ta haye gado. Ganowa yayi tsara shi kawai tayi don tsokana ya rinka binta yana cewa zaiyi maganinta tunda ya zama abin tsokana. Da kyar ya damkota suka fada kan gadon tuni idanunta suka raina fata da yace mata ya tuna yana da maganin yaji. Bai sake bari tayi magana ba ya hade bakinsu wuri daya yana jin yadda zuciyarta ke tsananin bugu. Don kansa ya kyaleta yana son su hada ido taki. "Ashe ma duk cika baki ne tsokanar taki. Nafi so idan kinyi tsokana ki shiryawa abin da zai biyo baya. Muje kitchen din nima ina jin yunwa idan mun dawo zaki fada min me da me aka fada miki da yasa kike tsorona haka har nake jin bugun zuciyarki yana neman fin karfin kwailan kirjin nan naki" Da muryar shagwaba tace "Ni dai ba kwaila bace" "Mu gani" ya fada yana dago hannu ta tashi a guje ta fita. Dariya yayi yabi bayanta sai dai dakin Gimbi ya fara wucewa. ***** Waya take yi yana tura kofar tayi saurin katse kiran. Tabe baki yayi yana girgiza kai. Tunda Rumana ta tare lafiya lokacin da zai mayar da yakinsa kan Gimbi yayi. Shi kadai yasan me yake kudurawa a ransa game da ita. Kallon banza tayi masa ta watsar duk kuwa da yadda zuciyarta take tsallen murnar ganin sa da jin kamshin turarensa mai sanyaya mata rai. "Uhmmmm angon kwaila me ya fito da kai? Nayi zaton ni da sake ganinka sai zaku asibiti nakuda ta kamata. Ko ka fito da ita goye a bayanka" "Me kike ci na baka na zuba. Muna nan dake wannan da abinda ya fishi duka zaki gani." "Ka dai ji kunya auren yarka...woooooo" ta rinka masa ihu. "Ke kinfi kowa sanin Rumana *halal dina* ce. Anyway nazo fada miki ne gas cooker dinki da wasu cikin kayan girkinki suna nan a gefe daya a kitchen. Kina da damar daukar duk abinda kike so a store ki dafa amma iya cikinki ke kadai. Ina rokonki tun muna fahimtar juna kada ki kuskura ki taba komai na Rumana" Wani daci taji a wuyanta na bacin rai. Ita da ta taba yiwa Rumana iyaka da kitchen dinta yau itace akayi mata iyaka dashi. "Dama maza da dama baku san adalci ba musamman idan kuka dauki budurwa. Kai naka gigin yafi na kowa ma tunda an hadaka da kwaila" Rike baki yayi tamkar baiji haushin kalmar da ta fada ba "Me? Idan ma Son So kike yiwa kallon kwaila kije a wanke miki ido. Matata duk inda ake bukatar mace ta kai har da kari...ai kin gane me nake nufi" ya daga gira yana mata murmushin mugunta. Ta kuwa hau ta cika fam ranta ya sake baci. Ta rasa yadda zatayi rayuwarta ta koma daidai. Hawaye taji ya sauko mata ta sharesu a fusace. Ta tsani Awaisu yana ganin hawayenta tamkar ta gaza ne "Kaga Malam kaje ka dafata ka cinye karewar soyayya amma ka dawo min da 'ya'yana gabana. *Banda rashin adalci da rashin sanin darajar haihuwa* me zai sa ka rabani dasu" Tafi Awaisu ya rinka yi ya shigo dakin sosai ya dawo gabanta ya tsaya "Gimbi ashe kinsan meye darajar haihuwa? Nayi zaton kinyi nisan da bakya jin kira. To bari kiji na fada miki " ya nuna ta da yatsa wanda ya kusa shigar mata ido "ni Awaisu Kabir Fika nasan daraja da kimar da Allah Yayiwa mahaifiya. Shiyasa dana dauke yaran na kaisu gidan iyayenki. Gimbi ko a lahira bana fatan su Haris su taba sanin matar da tafi kowacce mace daraja a rayuwarsu ta taba yin shirka, ta taba taka kafafunta taje gidan boka. Ni shaida ne kina cikin matan da suke matukar wahala wurin haihuwa musamman ta Mu'allim na kuma gode Allah babu haihuwar da kikayi ina nesa. Ciki da rainonsa da haihuwa duka babu wanda bansan yadda kika yishi ba. Wannan darajar ita tasa har yanzu kike amsa sunan matar Awaisu dan Maamu. Ke da na kai naki wurin naki iyayen kike jin haushina ki tuna abinda kika yiwa matar da baki san da yadda ta haifi nata dan ta raineshi ba." Idanunsa a lokacin sun kada sosai sunyi ja yana kukan zuci saboda tuna halin da Maamu ta shiga bai sani ba. "Har yau ban ga alamun nadama ko dana sani a tattare dake game da hakkin uwa da danta da kika daukarwa kanki ba. Bana jin zaki taba fahimtar halin da kika jefamu sai kin wayi gari matar daya daga cikin yaranki ta gasa miki wulakanci kwatankwacin yadda kika yiwa Maamuna" A zafafe tace "Allah Ya kiyaye wallahi wannan mugun fata naka ka gani a kanka" Lebensa ya dan cije "ai na riga na gani Gimbi tunda na aureki. Ke naki jiyewa dai kinsan duniya tamkar gona take. Abinda ka shuka shi zaka girbe. Mutum bazai shuka dusa yazo ya girbe ciyawa ba....kiyi tunani" Daga haka ya fita daga dakin yana tuno wasu lokuta da yake ganin Maamu a wulakance amma baya iya magana bare daukar mataki saboda an kawar masa da hankali. Gimbi kuwa jikinta ne ya hau bari babu gaira babu dalili ta kama kofar dakin ta rufe tana fizgar kanta saboda yadda taji duniyar tayi mata zafi. Ina zata ga Anti Bebi ne? ***** Rumana tana blending din kayan miya Awaisu ya shigo sai dai babu wannan fara'ar a fuskarsa saboda yadda ransa ya baci. Daga bakin kofa ya tsaya ya harde hannuwansa a kirji. Kallonsa tayi ta kula da yanayinsa wanda ta tabbatar dakin Gimbi da yaje ne ya mayar dashi haka. Tana son tambayarsa me ya same shi ta tuna da nasihar Mama da take cewa kada ta taba saka kanta a tsakiyar matsalarsa da Gimbi. Komai wuya komai dadi uwar 'ya'yansa ce saboda haka duk abinda ba'a saka da ita ba ta dauke kai sai taji dadin rayuwar gidan miji. Shiru duka suka yi na yan mintuna har ta juye kayan miyar a tukunya ta dora akan gas cooker dinta. Hantar da ta fitar daga freezer ta dauka zata yanka sai ta sake kallonshi ta dora hannuwa biyu a kanta. "Nayi mantuwa" Karasowa yayi cikin kitchen din yana kallon yadda take bata rai. "Me kika manta? Mu gyara kafin ki hada mana jagwalgwalo" "Attaruhu goma Iman tace na saka na manta na sa tara yanzu yaya zanyi da dayan?" Yana kallonta tana gimtse dariya yayi murmushi "Son So kin mayar dani kakanki ko amma nasan maganinki. Shi guda dayan da kika manta na yarda ki tauna ki zuba shi a ciki....bude bakin...haaaa" ya nufota da shi a hannu ba shiri ta fara bashi hakuri tana neman hanyar fita ya tare. Cikin dan lokaci ya ware suna dariya wayarsa ta soma ringing. Nuru ne yake kiransa ya sanar dashi suna hanya da matarsa Kubra zasu zo. "Baki zamuyi su Nuru da matarsa kin ganesu ko?" Ta gyada kai tana murmushi. "Sun kusa isowa kije ki dauko hijab ki ajiye a kusa" Fita yayi tabi bayansa da kallo tana jin wani irin yanayi mai cike da ni'ima idan tana tare da shi. Bata taba zaton hankalinta zai kwanta da auren nan ba sai gashi tun ba'aje ko'ina ba zuciyarta tana son tabbatar mata da cewa Uncle Awaisu ya cancanci ta kira shi Son So ba don ya dage sai ta kira shi da sunan ba. Kirjinta ta dafe saboda yadda zuciyarta take bugu da karfi. A hankali tace "Washhh zuciyata....Uncle kada kasa min heart attack" Juyo da ita taji anyi har ta firgita saboda tasan ita kadai ce a kitchen din. Fuskarta yake kallo yana kokarin kallon idanunta ya soma magana a hankali yana rungume da ita "Me ya sami zuciyar taki?" Kasa bashi amsa tayi saboda matsananciyar kunyar da take ji ta soma sunne kai. "Umm Ruman ki bani amsa please....kin bani wurin da nake son samu a cikinta ne?" Fuskarta kawai yake kallo ya sanya hannunsa a saitin zuciyarta mai bugu da mugun sauri. Hannunta ya kama ya dora a nasa kirjin har lokacin idanunta a rufe amma tana jinsa. "Idan baki yi min magana ba ni a yanzu heart attack din zai kamani" Zancen zuci ta kama yi tana yiwa kanta fada yaya akayi tayi magana da karfi har yaji. Suna wannan yanayin sai kaurin kayan miya suka ji ya saketa da sauri taje ta kashe. Zai sake magana suka ji kararrawa tana cewa _assalamu alaikum_. Sai da yaje bakin kofa ya juyo "Ina binki bashi" Ya kuma juyawa Rumana tace "Uncle..." ya sake waigowa sai kawai tayi masa wannan alamar ta _I love you_ da hannuwanta hagu da dama. Baki bazai iya kwatanta yadda yaji a zuciyarsa ba wannan lokacin. Yayi taku biyu da nufin dawowa gareta kararrawar gidan ta sake sallama yayi guntun tsaki su Nuru dai basu iya zuwa ba. Sai da taga ficewarsa hankalinta ya kwanta ta bi bayansa tana dafe da kirji. Dakinta ta wuce ta sako sabon dogon hijab ruwan kasa mai hannu har kasa ta sake komawa kitchen. ****** Da sallama ta shiga falon dauke da tray wanda ta doro musu juice mai sanyi da cake. Kanta a kasa ta gaishesu don duka kunyarsu take ji musamman Uncle Awaisu. Su Nuru kuwa suna janta da tsokana ta kasa sakewa. Awaisu ya kula a takure take yace su shiga dakinta da Kubra. Da saurinta kuwa ta mike suka tafi. A dakin ma dai a saliharta ta fitowa Kubra. Da yake babba ce kusan sa'ar Gimbi tasan yadda zata bi da Rumana. Da wasa da dariya ta rinka janta har ta sake. Kusan minti ashirin sukayi sannan Nuru ya kira wayarta yace ta fito su tafi. Ledar hannunta ta mikawa Rumana. "Ga wannan amarya ki tabbatar yau kika fara sha. Yana da kyau sosai in sha Allah zan rinka baki abubuwa masu amfani. Ki daukeni kamar Antinki ko yaya kinji" Rumana hannu na rawa ta karba tana ji Kubra na cewa ta saka a fridge dinta tunda akwai a dakin. Jikinta a sanyaye suka rakasu har bakin mota tana tsoron me Kubra ta bata. Dama saboda sakon Kubra ta nace sai taje gidan a ranar. Itama saya tayi wurin kawarta Maman Farida shine ta kawowa Rumana don tausayinta take ji. Yarinya karama girma ya hauta. Awaisu na rike da hannun Rumana ya kira drebansa ya bashi kudi ya siyo musu abinci. Suna gama cin abincin wanda ya siyo har Gimbi aka kira shi ba don yaso ba ya fice bai dawo ba sai da akayi Isha. ***** Kafin lokacin Rumana ta sake fitowa dora abinci ta ga Gimbi ta dasa kujera a kitchen din ta zauna. Ko bari ta ganta bata yi ba ta lallaba ta koma dakinta. Duk abinta tana tsoron duka wanda ta tabbatar idan Gimbi ta damketa to kashinta ya bushe. Awaisu kamar ya sani ya dawo gidan da abinci. Dakin Rumana ya ganta a kwance yayi mata murmushi. "Sorry na barki ke kadai uzuri ne ya taso min" Tashi tayi tana masa sannu da zuwa yace ta kashe komai na dakin ta taho dakinsa. Kafin ta iya amsawa yayi gaba. Wani guntun zazzabo ne taji yana barazanar kamata. Ina ita ina zuwa dakinsa a daren nan. Ita fa tunda gari ya fara duhu tsoro ya sami gurbin zama a zuciyarta. Kamar dazu da rana abinci ya mikawa Gimbi saboda baya son ko kadan ya shiga sahun masu tauye hakki sannan ya wuce yayi wanka. Ya kusa rabin awa babu Rumana babu dalilinta. Katan din su viju da juice da ya siyo mata ya dauko daga mota ya shiga dakin dasu. Tana takure akan gado jin ya taba kofar ta tashi a guje zata shige toilet harda bigewa da gefen gado ta saki kara amma duk da haka bata tsaya ba. Kansa kawai ya girgiza ya bude karamin fridge din ya fara jera mata lemukan. Dama saboda zuwa makaranta ne ya siyo mata. Karamar jarka ya gani da wani abu kamar zuma ya dauko ya kare masa kallo sannan ya fice ya tafi nasa dakin dashi. Ita kuwa wanka tayi saboda zaman bandakin ya isheta. A hankali ta leko ganin baya nan ta fito ta shirya cikin kayan baccinta ta haye gado ta kwanta tana fargaba kada ya dawo. Da Awaisu ya gaji da jiranta ya dawo dakin sai ya ganta tana bacci. TV din da ta bari a kunne ya kashe ya koma dakinsa yaci abinci yana tunanin Rumana da ta kwanta bata ci komai ba. Shima da kyar ya iya bacci yana ta tunanin maganganun da sukayi da ita a kitchen yana murmushi. Maganar Malamin da yaje ya gani ne ta fado masa tunaninsa ya karkata kan Gimbi har bacci ya dauke shi.*KASHE FITILA*💡49 *Batul Mamman*💖 Ana kiran assalatu ya farka yayi alwala sannan yaje dakin Rumana ya tasheta. A firgice ta tashi duk a tunaninta bata dade da kwanciya ba "Uncle yanzu zan taho" Gefen fuskarta ya shafa yana kallonta cike da so "kin yiwa kanki, kwana bakwai din da aka baki kin cinye uku a gudun miji. Ki tashi kiyi alwala asuba tayi" Maganarsa ta farko tasa ta jin kunya amma jin yace asuba tayi ya sanya jikinta yin sanyi. Tsoro take kada ya fara ganin kamar tana masa gardama ne. Fita yayi gidan da yake jikin nasa akwai masallaci nan suke sallah dayawa mazan unguwar. Da ya dawo dakinta ya sake komawa ya sameta akan abin sallah. Tana ganinsa ta gaisheshi ya mika mata hannu ta tashi tsaye. Gani tayi kawai ya rungumeta yana shafa kanta dake kwance a kirjinsa "Jiya kin barni ina ta tunaninki da kyar nayi bacci. Naso in fada miki yau zaki fara zuwa sch na tarar kinyi bacci" Kanta ta kara turawa jikinsa a hankali tace "kayi hakuri" "Its ok gobe sai kije. Ni zani office muje ki tayani shiryawa" Hannunta yaja ta bishi cikinta har wani kadawa yake yi. Ta tayashi shiryawa fa yace. Ita kam yau taga boni ta fada a zuciyarta. Suna shiga yace ta dauko masa tawul a toilet ta wuce ta dauko yana binta da kallo. Da zata bashi hannunta har rawa yake yi ta rufe idonta ta mika masa saboda tana fitowa ta ga yana cire jallabiyar. Hannunta ya riko da tawul din "muje ki tayani kada na makara" Ai tuni da bude idanun a rikice "Wa? Ni din?? Don Allah Kayi hakuri" Wuceta yayi yana cewa "lokaci ne dai nima zanyi miki yangar nan" ya shige bayan ya fada mata ta ciro masa kayan da zai saka. A iya saninta suit yake sawa idan zaije aiki. Bude wardrobe dinsa tayi ta gansu kala kala an jeresu makale a hanger. Guda daya ta dauko dark green tayi sa'a kowanne akwai matching shirt da tie shiyasa bata bata lokacin nema ba. Turaruka ta samu a kan dressing mirror ta fesa wannan ta fesa wancan a jiki. Jin motsin kofa yasa ta koma bakin gado ta zauna tare da rufe ido harda janyo hular kanta ta sake rufewa. "Allah idan baki bude idonki ba zamuyi fada. Don ma kinyi sa'a ina sauri bance muyi wankan tare ba" Wani yawu ta hadiya ta bude idon amma ta kasa daga kai. Da sauri sauri taga yana shiri kanta a kasa ita dai har ya gama. Kayan da ta dauko ya saka ta dan dago kai tana juya hannuwa "Uncle...uhmm Son So me zan dafa maka kaci kafin ka fita?" "Kada ki damu ina da uzuri ne da sassafen nan zan sha tea a office idan na nutsu. Ke dai ki tabbatar kin sami abinci kinci zan turo miki na rana sai na taho da dinner idan na taso. I may be late amma kiyi hakuri zan kira ki. " Kai ta gyada ya nuna mata kumatunsa ta dan daga gira alamar rashin ganewa yace "goodbye kiss" Gani yayi zata kuma sunkuyar da kanta yayi saurin dago habarta "please Son So i need it, kuma kinsan sauri nake yi dai" Rufe ido tayi yace yaga alama makauniyar Awaisu zai koma kiranta. A hankali ta matso harda dagenta sai dai lips dinta na karasowa ya juyo da fuskarsa sosai tayi masa a baki maimakon kumatu. Kunya sosai taji shi kuwa ya rinka dariya ya rike kugunta suka fita tana dauke da briefcase dinsa. Daga falo yace ta koma baya so ta fito a haka. Daga masa hannu ta tsaya yi har ya fice sannan ta koma dakinsa ta hau gyara. ***** Yana shiga mota yace da Gambo drebansa su wuce police station na zone 4. Da zuwa ba bata lokaci bayan ya gabatar da kansa aka kaishi wurin D.P.O. Bayan sun gaisa yace da Awaisu dalilin wayar da yayi masa jiya sun ga mota wadda ta dace da kwatancen motar matarsa da yace an dauke. Waje suka fita kafin ma a bude motar ya tabbatar ta Gimbi ce. Ciki suka koma a gabansa aka kira mutumin da ya saya shi kuma ya sake jaddada musu ba sata yayi ba da kudinsa ya saya. Nan dai aka nemi ya fadi a inda ya saya ya basu kwatancen gidan Ovi. DPO ya tabbatarwa Awaisu zasu je kamasu idan sun kawosu station za'a neme shi. Jikinsa a sabule ya fita yana fatan Allah Yasa Gimbi ba da kanta ta bada motar ba saboda ta sami kudin zuwa wurin boka. Haka ya wuni ranar baya jindadin aikin ga tunanin Rumana da ya addabe shi. Wuraren la'asar bayan Gambo ya dawo daga kaiwa Rumana abinci mutumin da Awaisu ya tura neman Anti Bebi ya kira yace bai sameta ba a Niger din da akace musu ta tafi. Inda aka kwatanta masa yaje wurin wani tsohon malamin tsibbu ne amma ance ta dawo Nigeria kwana biyu da suka wuce. Godiya yayiwa mutumin ya aje wayar. Nemanta yake yi dama saboda ya hadata da Gimbi ya kaisu gaban malamin da Nuru ya rakashi wurinsa. Mutumin babban limami ne a garin Abuja wanda ya tabatarwa da Awaisu idan suna son rayuwarsu ta tafi cikin kwanciyar hankali batare da fargabar wani sihiri ko cutarwa daga Gimbi ba sai ya kaita anyi mata nasiha da wa'azi da dukkan wani abu da za'a iya yi domin tsoratar da ita laifinta da azaba da kuma kwadayin rahamar Allah. Sosai ya gamsu da bayanin malamin saboda ko ba komai Gimbi uwar 'ya'yansa ce. Baya fata wannan halin nata yayi naso ya taba masa zuri'a. Shida da rabi ya isa gida ana gab da kiran magariba. Alwala kawai yayi ya fita. Kafin ya dawo Rumana tayi sallah ta fito falo jiransa. Kwalliya tayi kamar yadda Fattu ta koya mata tana sanye da riga da skirt na material ta rike dankwalin a hannu saboda yaki daurowa. Gimbi ce ta fito ta watsa mata mugun kallo Rumana ta dauke kai. "Wato kinyi aure kin girma shiyasa bazaki iya gaisheni ba ko" Kamar tayi shiru sai dai tace mata ina wuni. Kwalliyar da tayi da komai nata suka tsayawa Gimbi a rai. Duk wannan wai mijinta Awaisu Rumana tayiwa ya gani yaji dadi. "Rumana ki taimaki kanki ki bar gidan nan tun ban lahanta ki ba. Ki bar ganin na kyaleki har kinkai wannan lokacin. Duk ranar da na waiwayeki banajin za'a sake samun mamora a tare dake. Banza 'yar gidan masu zuciyar kare makwadaita" Rumana taji zafin maganar sosai ta tashi ta kalli Gimbi "karo na karshe da zaki sake zagar min iyaye kenan na kyaleki." Gimbi ta hayyako mata a fusace "nice kike kyalewa? Lallai Rumana bakya kaunar kanki shiyasa bakinki ya bude saboda kina ganin mun zama sa'anni mijinmu daya amma zanyi maganinki ina zuwa...." Ciki ta koma ashe kitchen ta shiga. Rumana tana tsaye zuciyarta na radadin zagin da akayiwa iyayenta sai ji tayi an kwara mata wani abu da bata gane ko meye ba da farko. Jikinta ne ya hau bari ganin danyen manja yana binta tun daga kanta har kafa. A daidai lokacin Awaisu ya shigo idanunsa suka gane masa Gimbi da galan din manja ga Rumana a tsaye ta gama baci. Ya harzuka karshe ya karaso gabansu sai dai ko kala bai cewa Gimbi ba zuciyarsa kawai ke masa zafi. "Son So tsaya a nan ina zuwa" Dakinsa ya tafi sai gashi ya dawo da roll din tissue har uku. Ya wuce kitchen ya dauko leda sannan ya tattare hannun rigarsa ya fara goge mata jiki yana rage manjan. Kuka take son yi amma ya makale jikinta ne kawai yake rawa. A zuciyarta tace dama me take tsammani daga Gimbi. Sai da ya karar da tissue biyu da kusan rabi yana goge mata jiki da wurin da take tsaye sannan ya dauketa har lokacin tamkar babu Gimbi a wurin suka shige dakinsa. Bai sauketa a ko'ina ba sai cikin baho ya tara ruwan zafi a bokita yace mata yana zuwa. Kofar dakin ya sakawa mukulli ya rufe sannan ya cire rigarsa daga shi sai dogon wando da ya nade zuwa gwiwa ya koma bandakin. ****** Wata irin kururuwa Gimbi tayi ta saka kuka mai cin rai. Ji take kamar son Awaisu zai kasheta. Wannan wulakancin da tayiwa Rumana tayi ne kawai don ya kulata ko fada ne yayi mata taji dadin muryarsa. Wannan wace irin masifa ce take masa so fiye da wanda take yi masa a da. Kuka take sosai tana rike kirjinta da yake zafi sosai. Daki ta koma ta shiga laluben numbar Ovi. Tayi sa'a 'yan sandan da suka je kamasu basu samesu a gida ba suna kasuwa taje sayar da sarkar gwal din da Gimbi ta kaiwa boka. Suna gudun tusar nan ta dafeta ko bokan bai sani ba. Kuka Gimbi takeyi kamar ranta zai fita. "Ovi kece gatana ki taimaka ki fada min yaya zanyi da rayuwata. Kullum son Awaisu tamkar ana hura wuta nake jinsa ga wannan tsinanniyar yarinyar ya fifita ta akan komai" Ovi taja gajeren tsaki ita fa Gimbi ta isheta ta hanata sukuni. Karya kawai ta sharowa Gimbi da sawa ranta zata jefar da sim card dinta ta sake wani. Idan sun sayar da sarkar gida zasu sake gabadaya ta nemesu ta rasa "Boka yace matar nan da akayiwa aiki na karshe itace nata aljanun suka hana komai yiwuwa. Yana tsammani itama boka gareta mai karfin gaske" Gimbi tayi shiru tana tunani. Tabbas biri yayi kama da mutum. Lokaci lokaci sai taji ana ja mata gashi ko ta kwanta a makureta akan gado. Abubuwan dake faruwa da ita sun wuce hankali ashe itama likitan 'yar hannu ce shine ta tona mata asiri a asibiti? Murmushi tayi ta ajiye wayar. Abinda tasan inda zata sami Dr. Yana. Komai zaizo mata da sauki. Iyaka dai ta bata hakuri akan ramuwar da tayi na bata mata aiki da Yana tayi duk da bata san me aka raba Yana din dashi ba. ***** Inda ya barta a tsaye haka ya dawo ya sameta. Tausayinta fal a zuciyarsa ya fara kokarin cire mata kayan da suka gama baci da manja ta rike masa hannu. Fuskarta ya kalla idanunta suna kyallin hawayen da yake barazanar sauka a kowane lokaci. Kai ta ga ya girgiza mata "Umm Ruman kada kiyi min gardama kuma kada kiyi kuka kinji ko. Raina a bace yake fiye da yadda kike zato. Kokari nake na danne fushina saboda bayyana shi bashi da wani alkhairi. Biyayya da hakurinki shine zai bani strength din cigaba da daurewa" Jikinta ne yayi sanyi sai ta koma tausayinsa ba ita da Gimbi tayiwa aika-aika ba. Duk da yanayi da suka tsinci kansu na tsantsar bacin ran da Gimbi ta kunsa musu bai hanata jin matsananciyar kunya ba. Tun daga kanta Awaisu ya soma wankewa sai da ya kusan karar da sabulu guda saboda yadda manjan nan ya sami wurin zama a cikin gashinta. Yafi rabin awa yana wanke mata jiki bandakin kansa ya fita hayyacinsa da mai sannan da ya gama yace tayi alwala ta jirashi a dakin. Kafin tayi alwalar ya fita tana gamawa ya dawo ya rufa mata tawul ya kaita daki sannan ya rufe kansa a toilet din. Sai a lokacin yaji wani hawaye mai dumi ya sauko masa. Zuciyarsa ta karye sosai daurewa yayi a gaban Rumana. Tuhumar kansa yake yi ta yaya akayi ya kwashi shekaru tare da Gimbi bai san haka zuciyarta take ba. Dubban mata sunyi abinda yafi watsawa kishiya manja saboda kishi, ya tabbatar ita ba kishin bane kawai a ranta. Son zuciyar da tayi ne yake bata masa rai ace maimakon nadama sai kara botsarewa take yi. Ashe kaddara bata fi karfin kowa ba. Duk inda kaji aure ya lalace sau tari ma'auratan suma sunyi zama na soyayya da yarda da juna. Sai wani tsatsayi ya gifta kaddarar rayuwarsu ta bayyana komai ya lalace. Har zuciyarsa yake jin wani irin tsoron Allah Yana kara shigarsa. Babu wayo fa babu dabara, kowanne bawa zai taka yaje inda Allah Ya rubuta masa. Yanzu da shi Allah Ya jarabta da son wani abin duniya har ta kaishi ga shirka don neman biyan bukata shikenan ya bata. Kenan idan kaga bawa a yanayi na sabon Allah ba tozarci bane ya kamata ya shiga tsakaninku. Addu'ar neman shiriya gareshi da nemarwa kanka kariya daga tarkon shaidan ya kamata kayi. Lallai Allah Ya soshi da Maamu bata mutu tana fushi dashi ba. ya tabbata da tuni sunansa ya dade da shiga cikin littafin tababbu wadanda sukayi asarar lokacinsu a duniya. Abinda ya jima baiyi da kansa ba yayi wato wanke bandakin sannan yayi wanka da alwala ya fito. A zaune ya tarar da Rumana ta takure jikinta wuri daya. Tana ganinsa ta sake matse jikinta yayi mata murmushi "Son So kwaila" Baki ta soma turowa "wallahi ni ba.....uhmmm... sai na fadawa Maamu" ta kare tana shura kafa. Murmushinsa ya fadada "ni kuma zan fada mata yau wanka ma don shagwaba ni kika sa nayi miki" Ai kuwa taji kunya don rufe kanta tayi da bargo ya rinka dariya. Ganinta kawai ya sassauta masa bacin ransa. Tana ta turjewa a haka ya shafa mata mai ya saka mata wata t-shirt dinsa mai girma tazo mata har kusan gwiwa. Duk tabi ta tsargu da yadda yake kallonta ta koma ta zauna har ya gama shiryawa ya sake fita. Ba jimawa ya dawo da hijab dinta da zani yace tasa suyi sallah yasan an idar a masallaci. Bayan sun idar abincin da ya siyo ya bata suka ci sannan ya koma gaban kujerar dake kallon tv a dakin ya zaune a kasa yace tazo. Da rarrafe ta iso don bata so ya ganta a tsaye. Fuskarsa ce ta dan sauya babu wannan fara'ar sosai sai alamun tausayi ya kama mata hannuwa ya rike. "Son So don Allah kiyi hakuri da abinda Gimbi tayi miki. Na rasa kalmar da zanyi amfani da ita na kawar miki bacin ran da kika ji dazu." Ko ba'a fada mata ba tasan yaji babu dadi saboda duka yanayinsa ya canja. Ji tayi itama ya kamata ta faranta masa kamar yadda yayi mata. Sai ta mayar da abin wasa. Matsowa tayi gabansa a kunyace "idan ka sake cewa nayi hakuri kukan da na boye zai fito na kwana ina yi" "To me kike so nayi miki kiji dadi ?" "Ka goyani" Gabanta yazo ya durkusa yaji shiru "hau mana" Baya ta matsa "wasa fa nake yi" "In durkusa din kice wasa kike yi, bazan yarda ba" Gani tayi da gaske yake ta dauki zaninta tace masa zata je ta kwanta. Yace daga ranar duk girkinta a dakinsa zata kwana. Da gaske tsoro ne ya kamata ta kama kofar zata fita ya soma magana "Yanzu har kin fara kin yin abinda nace? To jeki dakin sai da safe." Kawar da kansa yayi yana murmushi saboda yadda yaga jikinta yayi sanyi tsoron nata ya koma na gudun bacin ransa. A sanyaye ta dawo ta tsaya daga gefe "Kayi hakuri bazan kara ba" Zaune dama yake akan gadon ya nuna mata cinyarsa "zo ki kwanta muyi magana" Ba musu ta kwanta ta dora kanta a cinyarsa gabanta na faduwa. "Umm Rumana!" "Naam" "Ina so ki saurareni ba a matsayin mijinki ba. Ki dauki maganata daga bakin Uncle Awaisu. Gidan nan ba bakonki bane sannan Gimbi a gabanta kika karasa girma. Kinga yadda lamura suka koma tsakanina da ita duk da irin son da muke yiwa juna. Rayuwar aure is more than mata da miji suna kwana a daki daya ko gado daya. Rayuwa ce ta taimakon juna da rufawa juna asiri komai wuya komai dadi. Ko da wasa ban taba tunanin abubuwan da suke faruwa yanzu zasu ziyarci rayuwarmu ba sai gashi mun wayi gari a wannan yanayin. Shawarata gareki don Allah kada ki taba bari son zuciya ya kaiki ga aikata dana sani. Kina da hankalin sanin mene ne aure saboda haka idan kinga abu ya faru ba yadda kike so ba ni mijinki ne kiyi min magana ta fuskar da ya dace mu fahimci juna. Kada ki kuskura tsoron wani abu da bashi da tabbas ya kaiki ga afkawa haram " Maganganunsa sun tsaya mata a rai tunda ya fara take kuka. Nasiha sosai ya rinka yi mata saboda ya tsorata da yadda Gimbi ta rufe ido daga gaskiya lokaci guda. Yasan yanzu duk wani wa'azin da zaiyi mata bazata taba sauraronso ba ko don kishin Rumana. Shiyasa ya sami wannan limamin wanda yayi masa alkawarin yana dawowa daga tafiyar da'awa da ta kaishi Lokoja zai fada masa yazo da Gimbin gidansa. Kukan da Rumana take yi ne yasa ya fara shafa mata kanta wanda yake a jike har lokacin. A hankali rarrashin da yake mata ya juye zuwa soyayya mai wuyar fassara inda wannan rana ta kafa tarihi a rayuwarsu wanda bazasu taba mantawa ba. ***** "Sleeping beauty asuba tayi" shine abinda Rumana taji yana fada mata a cikin kunne. Motsin da tayi ne ya tuna mata da wahalar da tasha daren jiya ta sake kudundune jikinta tana hawaye. Dama sai da ya dawo daga masallaci ya tasheta don ko ba'a fada ba yasan yau kam akwai daru shi da Rumanansa. Dagata zaune yayi yana cewa ta tashi tayi wanka ga ruwan zafi can ya tanadar mata. Idanu a kumbure saboda tasha kuka bata ma san lokacin da tayi bacci ba ta mike sanye da rigar baccinsa wadda bata san lokacin da ya saka mata ba ta dan saci kallonsa suka hada ido. Murmushi yayi ta maka masa hararar da batayi niya ba a hankali tace " kuma na dena yi maka Son So" "Wanda nake miki ya ishemu" Baki ya rike yana kallo ta shige bandakin tana ta tura masa baki yabi bayanta tayi saurin saka mukulli ta rufe. Yace ta bude zai taimaka mata ne kawai tace ita ya barta zata iya. Dariya yayi yace mata yau zai karbi kowane hukunci amma tayi masa sassauci. Daga haka tashi yayi ya gyara gadon ya zauna jiranta. Tafi minti ashirin a ciki tana gasa jikinta kamar yadda Anti Umma yayar Mamanta ta fada mata ya kamata tayi. Da ta fito ko kallonsa batayi ba ita a dole tana fushi. Duk irin kukan da tayi masa bai tausaya mata ba bare ya kyaleta. A zaune tayi sallah tana idarwa taji yana dariya yana cewa aiki ya sami mata. Wani kukan ta soma ya zagaya gabanta ya zauna. Kunnuwansa ya rike yana kallonta "Tuba nake my sweet Son So bazan kara saki kuka ba. Kin hakura?" "A'a nima ba nayi ta rokonka ba kaki hakura" Shiru yayi kamar me tunani yace "to kada ki damu ki dauka kin kawo karar Son So wurin Uncle Awaisu ne zan miki maganinsa. Bulala nawa kike so ayi masa" Murmushi tayi saboda yadda yake tsokanarta. Wani baccin taji yana neman daukarta tace masa sai ta tashi zata fada masa. Akan abin sallan ta soma gyangyadi ya mayar da ita kan gado ya soma shirin fita. Yaso kwarai ace yau ba ranar aiki bace ya zauna ya kula da ita don niyyarsa sai ta gama jarabawa gabadaya ma zata zama cikakkiyar amarya sai kuma ya kasa. Bayan ya gama shirinsa takarda ya samu yayi rubutu ya ajiye mata a gefen pillow sannan ya fita. ****** Karfe goma ta dan wuce ta tashi jikinta ya danyi sauki ba kamar dazu ba. Ganin rana ta fito ta san ya tafi ko abinci bata bashi ba. Takaici ne ya kamata ta fara neman wayarta zata kira shi tace yau kada ya aiko mata da abinci zata dafa. Takardar da ya ajiye mata ta gani ta dauka tana karantawa tana murmushi son Uncle Awaisu yana kara shigarta. Sake karantawa tayi ta rungume takardar tana dariya ita kadai. *_I love you so much. Thank you for being mine._* Tashi tayi ta gyara dakin tas ta fita falo nan ma ta share tayi mopping musamman inda manja nan ya zuba. Dadinta daya ba kafet a wurin da tasan da wuya ya fita gabadaya. Tana aikin Gimbi ta fito dauke da handbag mai dan girma cikin shiri. Wani mugun bugun zuciya taji ganin Rumana da rigar Awaisu. Tunawa tayi da nasihar Awaisu da kuma rashin maganar da yayiwa Gimbi wanda ta tabbatar yana da dalilinsa na yin hakan sai kawai ta gaisheta. Ga mamakinta fuska a sake Gimbi ta amsa sannan tace mata ta tabbatar ta mori zamanta da Awaisu kafin ta dawo daga tafiyar nan da zata yi. Rumana bata fahimci kan zancen ba tace adawo lafiya ta cigaba da aikinta. Gimbi na fita ta dokawa maigadi harara ya matsa ya bata wuri yana daga mata hannu "a sauka lafiya Hajiya" Tsaki tayi ta wuce shi ta tsayar da taxi ta tafi tasha. Hankali kwance motar da zata Damaturu ta shiga tana kara rungumar jakarta. Babu komai a ciki sai kaya set biyu, kudin mota da takardun wani fili da Alh Mudi ya saya mata a Kano. Idan bokan Dr. Yana zaiyi mata aiki shine kadarar da zata iya bashi domin biyan bukata. Ita dai Awaisu ya sota ko da zai cika gidan da mata ya dauko duk danginsa na Fika.[28/08, 19:16] ‪+234 813 154 5123‬: *KASHE FITILA*💡50 *Batul Mamman*💖 *_A zaman tare yau da gobe sai Allah. Amma ina so a yau duniya ta shaida I realy appreciate duka matan Fikra musamman shugaba mai jajircewa Safiyya Ummu Abdoul_* *Masoyan KF a duk inda kuke wannan page din naku ne. Jazakumullah bi khair* Kafin azahar Rumana ta gama girki da gyara kitchen. Gidan ne taji yayi mata shiru da yawa kewar mutan gidansu ta kamata. Wayar Abba ta kira aka rinka zagaye sai da ta gaisa da kusan kowa har tana rokon Maamu akan ta dawo su zauna tare. Ta matsu lahadi tayi Awaisu ya dauko su Daula gidan ya dan farfado. Gashi sun rabu da Yusra kawarta bata da waya lokacin bare ta kirata yanzu. Awaisu ne ya kirata bayan ta gama waya da Iman yace zai turo dreba akwai kudi a dakinsa zaa kaita saloon a sake wanke mata kai sai tayi kitso. Godiya tayi masa kafin ya iso ta shirya. Wani hadadden wuri ya kaita duk ta tsargu saboda rashin sabo. Haka dai ta zauna aka gyara mata kan akayi mata kitso mai kyau. Sai laasar Gambo ya mayar da ita gida. ****** Kamar ta karbi motar tayi saurin kaisu Damaturu haka Gimbi ta rinka ji. Abin takaici sai magaribar fari suka isa. Daga tashar kai tsaye asibitin su Dr. Yana ta wuce tayi sa'a tashinta kenan zata tafo gida wata mai aikin shara ta rakata office dinta saboda tayi musu karyar yar uwarta ce ita kuma ta kasa samun wayarta. Dr. Yana tana kama hannun kofar office din Gimbi ma ta kama suka bude tare. Wata muguwar razana tayi cikinta ya duri ruwa ta koma ciki babu shiri. Gimbi kuwa tayi murmushi tare da shiga ta rufe kofar. "Wannan karon rayuwata kika zo nema ko me?" Dr Yana ta fada tana dan dakewa. Gimbi ta zauna ta dora kafa daya kan daya tana karkadawa "ko daya, kawance nake so mu kulla. Nasan komai game dake Doctor saboda haka mu manta da komai domin karuwarmu mu duka" A tsaye Dr. Yana take don bata san da me Gimbi tazo ba. Addu'a take yi kala kala a zuciyarta na neman tsari. "Ban fahimci me kike son fada ba" "Doctor kenan, kina zaton bansan ke kika turo min Gogojiya ba...sunan aljanar da take min aiki kenan idan banyi kuskure ba." Dariya tayi ganin Gimbi tazo mata da rainin hankali sai dai kuma tabbas tasan daga ina Gogojiya take. "Kina zaton kowa ma irinki ne mai nema daga wanin Allah?" Tebur din Gimbi ta dafa da hannuwanta biyu fuskarta a tamke "kinga kada ki munafurceni don nazo neman taimako wurinki. Idan ma aikin da nasa akayi a kanki ne ya bata miki rai ke kika shiga gonata gashi kinyi sanadin sake rabani da mijina. Yanzu haka Rumana yake aure wannan 'yar budurwar da sukayi zaman asibitin nan da babarsa" Sai a lokacin Dr. Yana tayi murmushi tana cewa ikon Allah yanzu Rumana tayi aure. Ashe hasashenta ya zama gaskiya. "Idan kin gama murna da bakincikina sai ki saurari me ya kawoni" "Baki isa na saurareki ba malama. Ni da kikayi sanadin rabani da abinda yafi komai soyuwa a gareni" Gimbi tayi dariya "munyi draw inji 'yan ball. Anyi 1-1." Ranta ya soma baci tace "kanki daya kuwa? Ki sa nayi barin cikin da na kwashe shekaru ina jiransa sannan kice wai munyi draw?" Hawaye ne ma ya sauko mata. "Kizo ki fita kafin na kira miki security" Jikin Gimbi ya danyi sanyi jin cewa bari Dr. Yana tayi ta dan sassauta murya "kiyi hakuri nayi zaton kema rabaki akayi da mijinki kamar yadda akayi min. Yanzu da kika ganni babu wanda yasan na taho. Mutumin da yake min aiki yace Gogojiya tafi karfinsa kuma ta hana ayyukana kama Awaisu. Shine nake so ki kaini wurin naki. Da shirina nazo ko me yake so zan bayar a mallaka min mijina" Ga mamakin Dr. Yana takardun fili Gimbi ta nuna mata. Tsoro ta bata don tasan lallai tayi nisan da sai anyi da gaske zata ji kira. Wayarta ta dauka ta turawa Mujahid dogon text tana masa bayanin Gimbi. Lokacin yana tare da Haj Fanta. Ganin ya tashi a firgice ta tambayeshi lafiya shine ya fada mata abinda Yana tace. Ta jinjina lamarin sosai tayi murmushi sai tace yaje ya daukosu da kansa a kawota Gimbi. Dan makotansu yasa ya dauko shi a babur tunda Yana da mota taje asibitin yaje ya daukosu. Sai lokacin da suka isa gidan hankalin Gimbi ya kwanta tana ganin hakkanta ya kusa cimma ruwa. ****** Da tunanin halin da ya bar Rumana a gida yake ta sauri ya kammala aikinsa. Ba don shine Manaja a bankin ba ya tabbatar yau da sai dai ya buga waya ya nemi alfarmar bazai je ba. Biyar saura ya fito yana ta sauri Gambo ya taso zai bude masa mota aka kira shi. Ko da ya duba DPO din da yake kula da case din wadanda aka kama da motar Gimbi ne. Ya sanar dashi cewa anyi nasarar cafkesu a hanyar zuwa kasuwa inda suke son ganin mai sayen sarkar Gimbin. Ba yadda zaiyi dole ya wuce station din bayan ya kira Rumana ya sake bata hakurin jinkirin da zai yi. Su Ovi ana zaune tsuru sun kasa gane mene ne yake faruwa sai ga mai sayen mota da Awaisu sun shigo. Yana ganin Rita ya gane fuskarta. Shi dama tuntuni ma ya tsaneta bare da ya dawo hayyacinsa ya tabbatar akwai abinda take yiwa Gimbi shiyasa ta barta a gidan. Kowa cikinsu yayi bayani inda su Ovi su so nuna taurin kai, sai dai bayan jikinsu ya fara fada musu sunci duka suka tabbatar wa 'yan sandan cewa motar suka sace Rita harda karawa da cewa akwai sarkarta a jakarsu saboda kada a sake dukanta. Ovi kuwa ta rinka harararta. Da sarkar da motar duka an bawa Awaisu kayansa sannan kudin mota kuma ance su Ovi zasu biya mutumin da ya saya tare da kara masa wasu kudin na tara saboda sun janyo masa zaman cell. A gajiye sosai Awaisu ya isa gida ga bacin rai sai dai yana ganin Rumana yaji hankalinsa ya kwanta. A bakin kofa ta tsaya da murnarta tun da taji ana bude gate. Tana ganin ya fito wata kunyarsa ta kamata sai ta tuna ai fushi takeyi dashi shine ta juya ta koma dakinta ta kwanta. Tsoron hada ido take dashi gara tace masa kawai tana fushi don ya kyaleta. "Son So rigima" taji yace bayan ya ajiye jakarsa yana sassauta daurin necktie. "Na dawo shine kika kwanta harda juya min baya ko" "Ban huce bane. Kuma na dena yi maka magana" ta fada har lokacin bayanta yake gani. "Yau a shirye nake kizo ki rama bazan ce komai ba...amma kafin nan a taimakawa bawan Allah da ruwan wanka na gaji." A hankali yake jan maganar ta sake lafewa taki tashi a shagwabe tace "ni ba cewa nayi zan rama ba" Shima muryarsa kamar zaiyi kuka yana kwaikwayonta yace "ni dai sai kin rama" Kamar ta shige cikin gadon don kunya sai murmushi kawai take yi. Shi kuwa don ta taso ya tuna jarkar da ya dauka a fridge dinta yayi murmushi zai tsokaneta "Naga wata jarka a fridge me kike yi da ita?" A gigice ta tashi jikinta yana rawa. Dama tsoron da taji kenan kada ya gani yace ko itama tana amfani da kayan asiri. Idonta har ya ciko da kwalla har ya soma zubowa "wallahi Son So matar abokinka ce ta bani kuma ko sha banyi ba. Nima nasan babu kyau" Daure fuska yayi ya zauna akan gadon "wato duk abinda na fada miki jiya kin watsar ko. An baki abu baki fada min ba" Kara tsorata tayi amma wannan Anti Kubra bata kyauta mata ba. Haka kawai zata janyo mata zargi. Durkusawa tayi a kasa kusa da kafafunsa tana share hawaye da bayan hannu "ba rokonta nayi ba, ban san ko na meye ba haka kawai ta bani. Amma yanzu zanje na zubar" Tashi tayi da sauri ta bude fridge ta nemi jarka sama da kasa ta rasa. Hankalinta ya sake tashi tana juyowa ta fada hannun Awaisu da yake tsaye kusa da ita. "Shikenan na yarda amma kada ki kara, muje ki tara min ruwa nayi wanka" Ba musu tace to don sauri ta rigashi zuwa dakin nasa ma. Yana biye da ita yana ta dariya a hankali. Tana fitowa daga bandakin ya sake daurewa "mata kuyi ta daukowa kanku abu mara amfani...anyway ki fiddo min kaya sannan ki jira idan na fito ki shafa min mai" Yadda hankalinta ya tashi sosai bata son fushinsa to ta sake cewa jikinta duk yayi sanyi. Indai zai hakura ko me yake so zatayi. Tana zaune ta rafka tagumi ya fito ya kusa kwashewa da dariya ganin yadda tayi saurin tashi tayo kansa da karamin tawul. "Bari na tayaka goge jikin nasan ka gaji" Kansa ta goge masa sannan ta dauko man zata shafa masa hannunta yana ta rawa ta kasa taba shi. Tausayi ta bashi ya dagata ya sauke akan gado. Hancinta ya ja yana kare mata kallo tayi kyau sosai cikin riga da skirt na atampa da ta saka "matsoraciya nima na rama abinda kika yi min shekaranjiya akan attaruhun indomin azaba" "Da gaske wasa kake yi?" Ta tsare shi da idanunta suna kyalli har yanzu da kwalla. "Tarkacenku ne na mata ta baki ko shima sai nayi miki bayani?" Kunya taji ta rufe idonta. Amma gaskiya ya tayar mata da hankali sosai don ba karamin tsorata tayi ba. Kafafunta ta fara bugawa tana masa shagawaba wadda take kara tafiya da hankalinsa "Ni sai na rama" Bakinsa ya kai saitin nata "dama ramuwar nake so kiyi tun dazu kin kasa fahimta" daga nan ya hanata tashi. ****** Suna isa gidan Dr. Yana da Mujahid suka yiwa Gimbi jagora zuwa dakin Haj Fanta. Tuwo take ci suka yi sallama ta amsa amma hankalinta yana kan Gimbi. "Sannu da zuwa Gombo" Gimbi ta kalli Dr. Yana ta murmusa "wato ke taki a gida take ma. Lallai kin ma fini. Gashi har sunana ta sani" Dr. Yana bata amsa mata ba don gani take da kyar idan Gimbi tana da hankali. Gaisawa suka yi da Hajiya sannan tayi musu alama su fita. Hankalin Gimbi a kwance tana ta jira matar ta bata damar fadin abinda ya kawota taji shiru sai cin tuwonta take yi. "Doctor tayi miki bayanin me ya kawoni ne ko har kin sani?" "Na sani shiyasa gobe da sassafe zamu wuce Maiduguri. A nan ne nake da wanda zaiyi miki maganin matsalolinki" Kayataccen murmushi Gimbi tayi "dama kuwa ina jin labarin Maiduguri suma ba daga nan ba wurin irin wannan taimakon. Yanzu ke sai a goben zan biyaki ko inda zamu je din zasu sallameki a abinda zan bayar?" Haj Fanta tace mata kada ta damu yiwa kai ne. Abinci tasa Dr. Yana ta kawowa Gimbi taci tuwo zuciyarta fes tana jiran gobe tayi maganin makiya. ***** Awaisu da Rumana na kwance tana ta shagwaba yana biye mata tace su tashi suci abinci. Kimtsawa sukayi zuwa falon ma tace ita bata da lafiya duka jikinta na ciwo sai kawai ya dauketa. A kujerar dinning table ya ajiyeta sannan ya zauna ta zuba musu farar shinkafa da ta dafa da sauce din hanta wanda yaji kayan lambu. Awaisu ya zuba santi don babu yajin nan irin na girkinta na farko. Lokaci lokaci tana kallon kofa ganin har tara ta wuce Gimbi bata dawo ba. Tana son fada masa amma tana tsoron kada ya zama gulma tayi kila ya riga ya sani ma. Bayan sun gama ya zauna yana kallon news tana kwance a jikinsa yana cewa ita da school sai monday ta zauna rabon kwana taki karatu. Dariya tayi amma hankalinta ba a kwance yake ba. "Son So me ya sameki ne? Da safe kinyi min gardama zaki iya kula da jikinki amma na kula kamar jan kafa ma kike yi. Tashi mu tafi dama nasan ba wani iya kula da kanki zakiyi ba" Da sauri tace "ni lafiyata kalau dama naga Anti bata dawo bane kuma ina tsoron yi maka magana ko gulma ce" ta tashi zaune. "Gimbi ta fita?" Ya fada ransa ya soma baci har muryarsa ta canja. Tsorata tayi dama haka take gudu. To amma dare yana kara yi shiyasa tayi tunanin fada masan shi ya fi. Fita yayi waje ya tambayi maigadi wanda ya tabbatar masa tun goman safe ta fice. Nan da nan kan Awaisu ya dau chaji. Wai me Gimbi take nema a rayuwarta ne? Ya tabbatar wurin wani bokan kila ta tafi saboda ta bari shaidan ya gama fitsare mata kai tayi nisa bata waige. Rumana na zaune ya dawo yace ta fada masa yadda sukayi da zata fita. Ita duk ta tsorata ma da yanayinsa ta fada masa abinda Gimbin tace. "Shikenan kije ciki ina zuwa" yace mata kawai bayan ta gama fada masa. Magana taso yi ya sake cewa ta tashi da dan karfi. Jiki a sanyaye ta tashi ga ciwon jiki da yake damunta wanda ya kara mata. Dakinta ta wuce ta je ta sami ruwa mai zafi ta zauna a ciki ko zata ji saukin jikinta. A hankali ta soma kuka tana tausayin kanta. Awaisu yayi ta buga wayar Gimbi tana shiga bata dauka ba. Hankalinsa ya kara tashi ya kira Alh Mudi ya fada masa. Ce masa yayi su jira zuwa wayewar gari. Tunda rayuwar da ta zaba kenan lokaci yayi da duka har shi zasu zare hannuwansu daga kanta. Shi dai haka ya ajiye wayar zuciyarsa tana zafi. Me zaice da 'ya'yansa nan gaba gamw da mahaifiyarsu don ya tabbata bazai taba bari ta kusance su yadda zasuyi sabon da zata koya musu mugun hali ba. Sai kai kawo yake yi a falon wayarsa tayi kara. Yana dubawa yaga Gimbi ce ya amsa da sauri. Lokacin ma Haj Fanta ce tace ta kira maigidanta ta fada masa tana lafiya tunda da bakinta tace mata babu wanda yasan inda take. "Naga kana ta wani kirana har amarcin ya kare ne? Kada ka fara murnar na tafi zaku sha iska dawowata daidai take da saituwar lamurana yadda nake so. Wannan yarinyar kuma tun wuri ka fada mata ta fara hada kaya watan zawarcinta ya kama" kit ta kashe wayar ko *a* bai sami damar fada ba. Ajiyar zuciya yayi tunda lafiya take bari ta dawo gidansu zata koma ya gaji haka. Rumana ce ta fado masa ya tashi yayi ciki da sauri. Fitowarta kenan daga bandakin daure da tawul idanunta sun kumbura sunyi ja. Bata san yadda akayi ba sai gashi a gabanta ya rungumeta. "Kiyi hakuri Son So nayi miki fada akan abinda bai shafeki ba" Dan ture shi tayi ta dago kanta. Sai lokacin ya kula da idanun "Subhanallah kuka kika yi? I am realy sorry bana son bacin ranki. Dazu na rasa tunanin da zanyi ne kawai nace ki tafi kada nayi abinda bazai miki dadi ba. Ashe ma na riga nayi" Ita dai bata ce komai ba har ya zaunar da ita ya tallafi fuskarta da hannunsa daya, dayan kuma yana wasa da yatsunta ya zauna daga gabanta. "I love you so much Umm Ruman. Kinga sakona da safe?" Kai ta gyada wata bakuwar kunya na shigarta. "Ina so ki zama mai hakuri da juriya akan rayuwa. Yadda na daga miki murya dazu bai kamata ba...." Girgiza kanta take yi saboda a ganinta bai dace mutum kamar Awaisu yana ta bata hakuri irin haka ba. "Ka dena cewa nayi hakuru ba fushi nayi ba fa ni bani da lafiya ne." "Bayar da hakuri yana da mahimmanci a zaman tare." Saitin zuciyarta ya dafa itama ya dora hannunta a nasa kirjin. "Yanzu kece nan dina nine nan dinki. Mun zama daya saboda haka kada ki rinka boye min duk abinda yake ranki. Ina reply din sakona na safe ko babu?" Ya tayar da ita zuwa gaban mudubi zai shafa mata mai. Murmushi tayi kanta a kasa "yana dakinka" "To muje ki bani" Turjewa tayi zata masa kuka "ni dai tsoro nake ji Son So ka barni a nan bani da lafiya fa nace" "Naji ai muje magani zan baki" Wani irin tausayinta yaji. Yasan yarinya ce dole sai yayi da gaske wurin lallabata. Sonta yake har kasan zuciyarsa baya son yana ganin hawayenta. "Bacci zamuyi idan kin nuna min reply din naga kin fara tsorata....I promise" ya kare da dariya Sai lokacin da saki jikinta ya taimaka mata ta shirya suka koma dakinsa. Haka suka kwanta yana rungume da ita a kunne ta rada masa "I love you Uncle Awaisu Son So" Nan ya manta da komai ya shiga karanta mata wasu darussan da bata san da irinsu ba a zamantakewar aure. ****** Kiran sallar farko ya tayar da Gimbi ta tashi ta ga Haj Fanta tana sallah. Alwala tayi da sallah amma a ranta tana mamakin ashe dai masu zuwa gun bokaye suna ibada sosai. Da sukayi wanka suka shirya Haj Fanta taci abinci amma ta fadawa Gimbi tun jiya sako yazo daga Gogojiya kada tasha ko da ruwa ne. Gimbi babu musu tace to tun yanzu ta fara jiyo kamshin sa'a a tafiyar. Da Mujahid da Yana suka tafi da yake sun fita da wuri goma a cikin Maiduguri tayi musu. Haj Fanta tasa ya kaita unguwarsu Yakura mahaifiyar Yana tace su tafi gidan daya daga cikin yayyensa mata su jirata. Duk su biyun suna son mata tambayar me zata yiwa Gimbi amma babu fuska. Kafin su sauka tasa Mujahid ya kira kanin Yana mai suna Bukarti ta karbi wayar cikin yaren kanuri ta kwatanta masa Gimbi da inda zai ganta sannan tace yasan yadda zaiyi ya sace mata jakar hannunta batare da ta kula ba. Gaban su Yana har faduwa yayi jin me tace ita kuwa ta matse abinta. Shiyasa suna ajiyeta suka wuce wurin Malam wanda yayi nasarar rabata da aljanunta. Da yake safiya ce unguwar babu mutane sosai Haj Fanta ta nunawa Gimbi wata hanya wanda idan aka mike zata kai mutum filaye da gonaki ne. "Gogojiya tace ki dora jakarki a ka sannan kiyi ta tafiyar minti ashirin babu waige a kan hanyar nan. Idan minti ashirin ya cika ki dawo nan inda kika fara sannan ki sake maimaitawa har sai inuwarki ta karkace tana kallon Yamma maso gabashin arewa" "Me kika ce?" Gimbi ta fada a rude. Sake maimaitawa tayi sannan tayi dan murmushi "aikinmu tamkar yankan wuka yake" Jikinta ya fara sanyi tace "to yanzu batun biyan fa" "Haba Gombo aljanun gaske ko kwandala bai kamata su karba ba. Su da suke bawa mutane sun fi karfin abin. Idan kin gama zaki ga wani yaro matashi zai kwatanta miki gidan da zaki sameni. Na barki lafiya " Gimbi na gani ta juya tayi gaba ta saita agogon wayarta ta fara tafiya. Ga rana ta take cikin dan lokaci ta fara gumi ga yunwa. Duk wanda yazo wucewa sai ta tambaye shi ko inuwarta ta karkata yamma maso gabashin arewa sai ayi mata dariya. Wurin shadaya da rabi ta tambayi wani mutum shi kuwa gani yayi kamar bata da hankali yace eh. Murna ta kamata ta sami wani tudu ta zauna kenan taga zugar samari suka rufo kamar zasu daketa kawai Bukarti ya sunkuce mata jakar da ta sako takardun filinta. Ihu ta rinka kurmawa ba jimawa sai ga wani yaro yazo bisa umarnin Haj Fanta ko magana baiyi mata ba ya kama hannunta suka tafi gidan Yakura. Ta gaji sosai kafafunta sunyi futu-futu suka shiga gidan. Haj Fanta ta gani da kanwarta wadda take ta yi mata fadan abinda tayi. Haj Fanta ta dago ta kalleta cikin bacin rai "Gombo kinyi babban kuskure da kika kawo kanki gidana. Nice mahaifiyar Mujahid mijin Yana wadda kika zubarwa ciki. " Yakura tace "haba Ya Fanta me zai sa ki biyewa jahila wadda bata san me takeyi ba har ki daukarwa kanki hakkin cutar da ita? Ke Gombo kike ko me fita ki koma inda kika fito" Gimbi ta tsaya turus tana kallosu. Me suke nufi? Duk wahalar da tasha dama karya ne. Ranta yayi masifar baci ga tsoro sai ga hawaye babu shiri. Haj Fanta ta harareta "au kuka kike yi tun yanzu? Baki ga komai ba a abinda nayi miki tanadi. Gogojiya kuma yanzu ta fara min wasan kura dake" "A gaskiya Fanta kin bani mamaki" Dukkansu ukun suka dago kai suna kallon Dr. Yana da Mujahid sai kuma wani farin dattijo mai shekaru. Fuskarsa ma'abociyar kwarjini da haiba ya hade yace a nuna masa inda zasu zauna magana ce yake so suyi. [28/08, 19:16] ‪+234 813 154 5123‬: *KASHE FITILA*💡51 *Batul Mamman*💖 Yakura wani karamin falo ta bude musu daga waje kofarsa take duka suka shiga suka zazzauna. Malam ne kadai akan kujera sauran kowa na kasa. Gimbi ya kalla a nutse ya soma magana bayan basmallah da korar shaidan. "Baiwar Allah Yaya sunanki?" Ba karamin kwarjini gareshi a idonta ba tace Gimbiya. "Na gaskiyar dai. Gimbiya ai ba suna bane" A hankali ta fadi sunanta yadda ko Haj Fanta da tafi kusa da ita bata ji me tace ba. "Sunanki mai daraja kuwa...ko zaki iya duba girman Allah ki fada min matsalarki batare da kinyiwa kowa karya ko sharri a cikin labarin ba?" Dan tunani ta tsaya kamar bazata yi magana ba sai kuma ta fada masa abubuwan da suka faro tun daga lokacin da Awaisu yace zai dauko Maamu da komawarta gida kafin su tare a sabon gidansu, zaman da tayi da Maamu, dinkewa da Anti Bebi da sakin da yayi mata har dai zuwa matsayin da suke a yanzu. Wasu abubuwan ta fada wasu ta sakaya. Malam yayi ajiyar zuciya yana gajeren murmushi "wato idan na fahimceki tsoron kada uwarmiji ta kashe miki aure yasa ki yiwa kanki rigakafi kika hau farautar farinciki da kwanciyar hankalinta a gidan danta." "Malam mata irin wannan Gombon wallahi annoba ne a cikin al'umma. Da Mujahid take aure da ta dade da komawa gidan ubanta..itama surukar taki ina tsamman asirin da kika yi mata bai gama sakinta ba" cewar Haj Fanta tana jin kamar ta hau Gimbi da duka don takaici. Yakura ce ta dan tabata alamar tayi shiru. Malam yace "barta tayi idan zamana ne bata so a nan din sai na tafi" Wannan karon Mujahid ne yayi magana "kayi hakuri don Allah" "To ku bani hankulanku nan muyi magana ta fahimta" duka kuwa suka koma fuskantarsa. "Tun duniya na kwance lokacin da abubuwa basuyi tsanani kamar zamanin yanzu ba kusan kowa a kowane bangaren duniya yasan da matsalar dake tsakanin uwarmiji da matar danta. Lokuta da dama mata sukan fasa aure idan suka tabbatar gida daya zasu zauna da surukai. Abin mamaki shine wannan rigima kusan iri daya ce a ko ina. *Kishi* ne mara tushe. Ita uwar miji tana ganin ta haifa wata bazata fita morar wahalhalun da tayi da danta ba musamman da tasan kaf duniya tafi kowa iko dashi. Mata kuma tana ganin mijinta ne dole ya sauke hakkinta dake kansa. Kowacce cikinsu tana da gaskiya sai dai duka suna mantawa da cewa matsayi daban garesu a rayuwar namiji idan kowacce ta tsaya a iyakar da Allah Yayi mata dangane da alakarta da mutumin to zata fi kowa samun nutsuwa a rayuwa" Gimbi ta dakatar dashi tace "Malam ba fa da ka nayi abuna ba. Labarai da yawa naji wasu kuma na gani da idona. Kusa da gidanmu kafin nayi aure uwarmijin a kofar dakin dan take zama har ya dawo komai dare idan da leda ta karba ta raba ko ma menene a ciki nata yafi yawa ta bashi sauran ya kaiwa matar da yaransu. Nawa mijin babana ne ya sama masa aiki kaga kuwa ni nafi dacewa da kyautatawarsa fiye da Maamu." Harara su Haj Fanta suka rinka maka mata Malam ya jinjina kai "idan da mata goma masu surukai zasu tsaya a wurin nan to ina da yakinan takwas cikinsu zasu miki korafi da uwarmijinsu. Baiwar Allah duk abubuwan da kika sani game da su bazan boye miki ba yawanci duka gaskiya ne to amma fa akwai abin da baku zurfafa tunani akai. Kowacce halitta a duniya baka rabata da kishi. Kuma yawa yawan kishin yana faruwa ne idan kika ga wani ko wata yana samun fiye da abinda kike tunanin hakkinki ne daga wurin wanda ake kishin dominsa. Uwa da kuke ji da gani daraja da kimarta tafi karfin wasa. Baku san ayoyin da Allah Yake cewa ayi da'a gareshi Yake bin wannan umarnin da cewa a kyautatawa iyaye ba. Shi kuma Annabi SAW ya tabbatar mana da cewa a iyayen ma uwa tafi uba cancanta da kyautatawa har sau uku? Cikinku wace bata san wahalar ciki, haihuwa da raino ba? Banda ke Yana muna da miki fata samu amma ana haifa a gabanki ko. Kina mace ki kare wannan wahalar ki dawo gidan danki sai ya baki daki kamar akurki a bayan gida yana ganin alfarma yayi mata. Ita da ta haifa ya tare jikin mata idan taci sa'a ya leko suka gaisa kamar yana kan kaya zai tashi yayi gaba. Ya koma rayuwa daga shi sai iyalinsa ita uwa ko iyayen duka biyu kuji ana cewa haka zamuyi ta hakuri dasu har a rabu lafiya. Allah sarki iyaye mutuwarsu kawai 'ya'yan ke jira su cigaba da fantamawa babu damuwar komai a ransu. Ana haka ko ba'a yi? " Jikinsu ya fara sanyi harda Gimbi kuwa suka ce anayi. Malam yace "to wannan dalilin ga kuma rikici na girma suna taimakawa wurin sanya uwarmiji takurawa surukai. Itama taji labari ko ta gani ya faru da wata sai tayiwa kanta rigakafi irin yadda kika yi" ya yi maganar yana kallon Gimbi. Shiru tayi tana tunanin rayuwarta. A iya saninta zata iya rantsuwa ko sau daya Maamu bata taba yi mata kallon banza ba tun kafin zuwanta Abuja. Kafin abubuwa su lalace ba ita kadai ba hatta Baaba Hure da 'ya'yanta basu taba saka mata ido ba. Wata zuciyar tace mata amma duk don suna son turo miki Maamu ne da 'yarsu ya aura. Kwanciyar maciji suka yi miki sai kin sakankance kiji harbi irin yadda suka so yi ba don kin taimaki kanki ba. Kallonta su Malam sukeyi ta zurfafa a tunani. Ta dago kai "yanzu kana nufin dai komai laifina ne, nayi ba daidai ba saboda na nemawa kaina da yarana 'yanci?" Wannan karon yaji ta soma bashi haushi ana ga yaki tana ga kura. "Baiwar Allah da kinsan girman zunubin da kika aikata bana jin zakiyi magana irin wannan. Duk duniya babu zunubin da ya kai shirka kuma kinyi. Manzon Allah SAW ya fada mana mu al'ummarsa cewa mu dage duk runtse mu mutu muna musulmai, saboda Allah mai rahama ne da jinkai yasan cewa indai laifi ba hakkin wani muka tauye kamar yadda kika yi ba to idan Allah Yaso duk tulin zunubanmu sai Ya yafe mana Yace mu shiga aljanna cikin rahamarSa. Duk wanda ya mutu yana mai imani da bokaye da malaman tsibbu mushirikine ko yaki ko yaso." Gimbi ta dafe kirji "A'a fa Malam ni ba imani nayi dasu ba tunda ina sallah ina azumi " Murmushi yayi mai ciwo da nuna bacin rai saboda masu bin bokaye da dama haka suke cewa su musulmai ne alhalin daga lokacin da ka yarda wanin Allah zai iya biya maka bukata to ka tabe kai da rahama sai ranar da kayi tuba irin wanda sharia ta aminta dashi. "Gimbiya! In tambayeki mana shin tunda kika shiga matsalolin nan kin taba daga hannu kin roki Allah Ya yaye miki a matsayin Ubangijinki majibincin lamuranki?" Nan ake yinta, tabbas bazata iya tuna yaushe ta kai kukanta ga Allah ba. Hasali ma sai yanzu ta farga cewa kullum fa burinta a sami bokan da yafi kowanne kwarewa a aiki. Jikinta a take ya fara rawa kamar mazari da ta tuna duk wata kadararta ta kare a gidan boka. Basmallah yayi yace " *WA IZA SA'ALAKA IBADI ANNI FA INNI QAREEB. UJIBU DA'AWATAD DAA'I IZA DA'AN. FALYASTAJIBULI WAL YU'MINU BI LA'ALLAHUM YARSHIDUN* " Ayar da duka suka ji Malam ya karanto kenan yana karewa sai hawaye ya ziraro daga idonsa daya. Daga nan fa kwakkwaran motsi duka sun kasa saboda firgici da tuna ayar Allah musamman wadanda suka fahimci me ya fada da larabci. Malam yace cikin murya da yanzu take nuni da bacin rai da son firgita mai sabo "Kina ina Allah SWT girma, da isa da buwaya sun tabbata a gareshi baShi da matamaki azza wa jalla sarki zuljalali wal ikram Yake cewa Annabi Muhammad SAW idan bayiNa suka tambayeka game daNi ka fada musu cewa Ina kusa...wannan kusancin ina mai tabbatar muku cewa Allah Yafi jijiyoyin dake cikin jikinmu suna gudanar da jini kusanci damu. Sannan yace Shi Ubangijinmu mai jin addu'ar mai roko ne idan ya roke shi. Saboda haka mu roke Shi kuma muyi imani daShi ko zamu samu shiriya. Na rantse da Sarkin da Ya busa min numfashi wannan ayar tana kwantar da hankalina da sanya nutsuwa a lokacin damuwa. Idan har bawa ya tuna wannan zance na Mahaliccinsa kuma yana ikirarin imani da musulunci to babu abinda zai dame shi ya kasa daga hannu ya kai kukansa inda za'a share masa hawaye." Idanun Gimbi a take suka shiga kwararar da hawaye masu zafin gaske. Malam kuwa cikin daga murya domin ya kara tada mata da hankali ya kori duk wani sauran shaidanci da yake yawo a zuciyarta ya cigaba da magana. "Kina da Ubangijin Annabi Muhammadu me ya kaiki wurin boka? Kina da Sarkin da gyangyadi bai taba daukarSa ba me ya kaiki wurin wanda ko yau ko gobe rana zata zo da za'a turmutsa shi a kabari? Kina da Mamallakin sammai da kassai wanda Yace da zai biyawa dukkanin bayinSa na farko zuwa na karshensu dukkan bukatunsu to babu abinda zai ragu daga taskarSa. Har Annabi SAW ya bamu misali da cewa kamar fa a tsoma allura ne a cikin makeken teku a tsamota. Kai mata! Kuna da Sarki mai _kun fa yakun_ me yake kaiku wurin kazaman bokaye a dazuka suna shiga tsakaninku da ganin hasken rayuwa? Bokayen da suke nema daga aljanu su kuma aljanun suke sata su basu ko kuma suje su yi ta sanya wasi wasi a zukatan bayi su farraka masoya su bata alkhairi su maye gurbinsa da sharri. Idan kura tana maganin zawo ya kamata bokaye sufi kowa kudi da samun manyan mukamai a duniya amma sai kiga mutum a jeji yace zai biya miki bukata amma sai kin biya wasu makudan kudade kin kuma bar ibada. Bayan kuma wanda Ya halicceki domin ki bauta Masa baYa gajiya da jin rokon bayinSa. Koda yake rashin hakuri shine babbar matsalarmu munfi son mu roka mu ajiye hannu tare da biyan bukata. Sai dai Allah Yafimu sanin me ya dace damu a kowane mataki na rayuwa. Shine mai biyan bukata take yanke sai dai Yakan jinkirta mana zuwa lokacin da amsawar adduar yafi dacewa." Zuwa yanzu ba Gimbi ba hatta Haj Fanta kuka suke yi sosai. Gimbi ta dafe kirjinta tana kiran ta shiga uku ta cuci kanta. "Muddin kina numfashi baki shiga uku ba domin kuwa addua bata barin komai" cewar Dr. Yana. "Ina so ku sani cewa rayuwa da mutuwa gaskiya ne kuma zaman kabari da busa kaho abu ne tabbacce da zai faru komai nisan lokaci. Gimbiya ki kiyaye ranar da zaa tona rami a kasa a sanyaki daga ke sai halinki Mala'iku su zo gareki domin amsa tambaya. Shirka bala'i ce, bokaye da yan tsibbu da matsafa duka masifa ne, sannan duk wata halayya da mutum zai tsira domin haddasa husuma tsakanin mutane ko da ba masoya bane halaka ce gareshi. Allah mai rahama ne da jinkai...ni da ku duka muna kyautata Masa zato da kwadayin ranar da Zai umarcemu da shiga aljanna mu rayu cikin ni'ima. Jahannama da Qur'ani da Annabi SAW suka bamu labarinta wuta ce da ko tururinta bazamu jura ba balle ita kanta. Kuma kada kuji da wai, ana gama hisabi zaa kawar da mutuwa babu wanda zai kara mutuwa. Rayuwa ce ta dindindin har abada. Ko ba'a tambaya ba nasan babu wanda zaiso yin yini daya cikin wuta balle rayuwa mara yankewa. Mijinki yana da rai sannan surukarki tana da rai saboda haka zabi ya rage naki" Kuka mai tsuma zuciya Gimbi take yi saboda tausayinta su Dr. Yana ma kukan suke yi. "Allah na tuba! Allah na tuba!! Malam yaya zanyi na kankare wannan masifar da na janyowa kaina da hannuna daga littafina? Malam yaya zanyi idan aka bani littafina ranar lahira a hannun hagu? Shikenan ni bani da rabo?" Zuciya a karye take magana cikin kuka. Haj Fanta ta janyota jikinta itama tana kukan. Shi kuwa Malam bai barsu haka ba ya rinka janyo hadisai da ayoyi yana cika musu zukata da tsoron shirka. Sunfi awa biyu a zaune sannan yace zai tafi. Gimbi ta rarrafa ta dan matsa kusa da kujerarsa "Malam yaya zanyi da iyayena, mijina da Maamu? Na yarda na rasa komai a duniya indai zasu yafe min na rabauta ranar lahira...wayyo ni na cuci kaina" "Ki kwantar da hankalinki ki yiwa Allah kirari da yabo da godiya sannan ki tuba. Gafarar Allah yawa gareta har Yake cewa da bawanSa zaizo masa da zunubi kamar kumfar teku kuma ya tuba , to da Zai zo masa da gafara kwatankwacinta. Mu duka masu laifi ne mu yawaita tuba ko zamu dace da gafarar Allah. Mu kiyayi manya da kananun kaba'ira bakin gwargwadon iyawarmu Shi kuma Allah Zai kiyaye mana imaninmu Ya tsaremu Ya saka mana da rahamarSa da muke rayuwa a duniya domin nemanta. Allahumma innaka afuwun kareemun tuhibbul afuwa fa'afu anna." Gabadayansu suka amsa da Amin suna goge hawaye. Malam ma yana fita nasa hawayen suka sauko na tsoron Allah yana mai jaddada addu'a akan yin nasara a zuciyar Gimbi. Haj Fanta kuwa hannun Gimbi ta kama ta kaita uwar dakin Yakura sannan da kanta taje ta zuba mata abinci ta kawo mata. Tana zuwa ta sameta a nan inda ta barta tana ta kuka har tana neman shidewa. Tunda tazo duniya bata taba jin tsoron azabar Allah kamar yau ba. Jin kanta take kamar wadda ta rayu cikin mafarki yau ne ta farka. Kusa da ita Haj Fanta ta zauna jiki a sanyaye "Gombo kici abinci sai mu fara tunanin komawarki gida" "Hajiya wane gida zani a yadda nake jin kaina lullube da kazanta? Kin san sau nawa kafafunnan suka kaini gidan boka? Sau nawa hannuwana suka yi amfani da magungunan bokaye domin cimma burina? Ku taimaka min muje na roki Maamu gafara wallahi idan ta yafe min nasan Awaisu zaiyi saurin yafe min shima. Ga iyayena sun dade da yin fushi dani. Ga Anti Bebi da nasa aljanu suka mayar da ita tamkar mahaukaciya" wani kukan ta saka Haj Fanta tayi ta bata hakuri. ****** Tun fitar Awaisu da safe Rumana ta gama gyara gida sannan tazo tayi girki saboda yace mata gida zai dawo yayi shirin zuwa sallar juma'a. Tana tsaye a gaban wardrobe dinsa tana neman kayan da zata dauko masa taji ya bude kofar dakin da sallama. A hankali ta amsa amma bata juya ba. Tana nan tsaye har yazo ya rungumeta ya rankwafa ya doro kansa a kafadarta. "Duk fushin ne my sweet Son So, gaskiya na kula mijin nan naki sarkin laifi ne amma nasan maganinsa" Juyawa tayi har lokacin yana rungume da ita ta turo baki. Tun asuba da ta tashi tana sallah ta tafi hada masa abinci duk da bacci da muguwar gajiyar dake damunta. Amma da ya fito kurba daya yayi wa tea tare da mata kiss ya fice yace yana sauri. Waya ce ya samu daga DPO cewa anyi masa waya daga sama ance ya saki Ovi da kanwarta. Ita kanta Ovi bata san hakan zata faru ba ta dai gwada sa'arta ne ta kira wani mai babban mukami da sukayi hulda a baya ta nemi alfarma shine yace a saketa. Ko da yaje sun gama rufe case din DPO ya bashi hakuri. Ransa a bace ya wuce office sai yanzu da ya dawo ne yaji dadi da yaga Rumanansa. Kallonsa tayi tana dan murmushi "to yaya aiki?" "Lafiya kalau sai gajiya da yunwa" Cikin shagwaba tace ita dai daga yau ya dena fita bai ci abinci ba. Yana rike da hannunta suka fita falo ta zuba masa yana ci suna hira. "Kinga dai korafi da mita ta kare na dawo naci abinci gashi har ina da sauran lokacin yin wasu abubuwan kafin nayi shirin masallaci" "Wani aikin zaka yi kuma daga dawowa?" Kashe mata ido yayi yana wani murmushi "eh mana..aikin kula da amaryata" A tsorace ta mike don ta fara fahimtar inda ya dosa. Ya damko hannunta kafin ta gudu "Ina zaki kuma muna hira matsoraciya?" Fuskarta kamar zatayi kuka tace "Son So bani da lafiya ne" Hannu yasa a kasan habarsa "ohhh yarinyar nan ba dai fassara ni kikayi ba. Don da kin fara kiran rashin lafiya nasan me kike gudu" yana mata dariya Tuni kunya ta kamata ta daure tace "ni dai babu abinda nake nufi, bance komai ba" Dariya yake sosai ya tashi tsaye yana shafar fuskarta da bayan hannunsa ya soma magana kasa-kasa "ni din me kike tsammani ina nufi uhmm?" Duk ta rikice ta rasa amsar bashi ya cigaba da tsokanarta har ta fara masa kuka. "Idan kaga amarya na kuka fa rarrashi take so, bari ki gani" daukarta ta ga zaiyi ta gudu daki tana dariya. Soyayya sosai da kulawa ya nuna mata sannan ya tafi masallaci. Da ya dawo a kwance ya sameta tayi sallah bacci ya dauketa. Shima kwanciyar yayi ya rungumota suka yi baccin tare. ****** Da kyar Gimbi ta iya shan tea da su Yakura suka takura mata sannan ta roki alfarmar a bata kudin mota Fika zata wuce. Sai lokacin Haj Fanta ta tuna da jakarta da tasa Bukarti kwacewa a hannunta ta mika mata sannan tace mata zasu tafi tare da ita saboda kada a ki gaskata ta. Murna Gimbi tayi ta rinka godiya kalmar da ta dade banda boka da Ovi babu wanda take fadawa. Daga nan ta roki su kaita wurin wannan malamin kafin ta tafi. Sai bayan masallaci suka je gidan nasa. Yana ganinsu yayi hamdala domin yasan canjin ra'ayi daga wurin Gimbiya shi kadai ne zai kawota gidansa. Shima godiya tayi masa sosai yayi ta mata addua har yake bata labari akwai kaninsa limami ne a Abuja kwana biyu kenan da ya kirashi yana bashi labarin wata matar manajan banki da abubuwan da tayi. Ya kare da cewa yanzu kanwar babarta kamar dai naki lamarin ita yake nema saboda itace ta koya mata bin bokaye. Ya kira ne dama yana neman shawarar yadda zaiyi mata nasihar da zata shigeta. Wani sabon kukan mai taba zuciya Gimbi ta soma tace "wallahi mijina ne, Malam ashe har yanzu bayan abubuwan da nayi Awaisu yana sona da alkhairi. Na cuci kaina na cuci mijina kuma naci amanar zaman tare da soyayyarsa gareni..gabadaya lamarin nan babu ta inda matsala ta taso min ni kadai na rinka kidana ina rawata gashi komai ya baci" "Kuma komai zai gyaru da izinin Allah. Kin dai ga yadda ikon Allah yake wanda kika so cuta yana binki da kishiyar abinda kika yi masa. Ina jin har duniya ta tashi baza'a dena samun sabani tsakanin surukai ba amma ki tuna Manzon Allah SAW yace kada mu cuci kowa kuma kada mu bari a cucemu. To idan har daya zai faru gara ki jewa Allah a matsayin wadda aka cuta akan kije a macuciya. Komai runtsi komai wuya kiyi kokari kiga baki cutar da dabba ba ma balle dan Adam kuma musulmi. Wanda duk ya cuceki Allah zai isar miki ko a gaban idonki ko bayan kin koma gareShi. Allah Yayi miki albarka Nana mai sunan manya" Tana kuka sosai tace Amin suka shiga motar Mujahid wannan karon harda Yakura suka nufi Fika. [28/08, 19:17] ‪+234 813 154 5123‬: *KASHE FITILA*💡52 *Batul Mamman*💖 Wuraren uku da rabi wayar Awaisu ta soma ringing. Saurin amsa kiran yayi tare da kwantar da kan Rumana a kan pillow ya fita don kada ya katse mata bacci. Ganin sunan Harisu da yayi yasa shi murmushi ya amsa suka gaisa. Zai fara jansa da hira ya katse shi ta hanyar sanar dashi zuwan Gimbi gidan tare da Dr. Yana da mijinta da wasu mata biyu. Mamaki ya kama Awaisu sai Harisu ya ce masa yayi kokarin tahowa ko zuwa da safe ne don tunda tazo banda kuka babu abinda take yi tace kuma bazata yi maganar abinda ya kawota ba sai Awaisun yazo. Hankalinsa a take ya tashi yana tsoron ko wani sabon salon makircin ne ta kulla. Alh Mudi ya nema a waya yayi sa'ar samunsa ya sanar dashi halin da ake ciki. Shima nasa hankalin ne ya tashi yana tsoron me Gimbi taje tayi. "Awaisu ni dai idan babu damuwa zan kira Harisu na fada masa a yau dinnan ba gobe ba zan tafi Fika na daukota. Lokaci yayi da zaka datse duk wata alaka da Gimbi don wallahi a yanzu ba iyayenka ba kai kanka kunyarka nake ji." "To abinda za'ayi Alhaji ku shirya har Mama idan zata iya zuwa da su Haris sai mu fito mu same ku drebana yaja mota daya nima naja daya. Sai dai kuyi hakuri zamuyi tafiyar dare kam" Alh Mudi yaji ya kara son Awaisu yace kada ya damu zai nemi kanin Gimbi yaja su shi yaja tasa su hadu a gidan mai na fita gari sai su wuce tare tafiyar bibbiyun zata fi dadi. Sun yanke shawarar haduwa nan da hudu da rabi. Dakin ya koma har lokacin bacci Rumana take yi. Yasan ta gaji tana bukatar hutu amma bazai iya tafiya ya barta ba gaskiya. A gurguje ya hada musu kaya shi da ita sannan ya tasheta yace ta shirya Fika zasu tafi. A tsorace take sosai zai dauki jakar kayan nasu ya kai falo ta riko shi "Don Allah me ya faru?" "Kin fiye tsoro Rumana babu komai in sha Allah. Ki shirya zan fita nayi sallah ina dawowa horn zanyi miki. Ga keys nan ki kulle ko'ina" Ai sai kawai ta fashe da kuka, gani take wani abu ne ya faru baya son fada mata. Idan ba haka ba me zaisa da yamman nan haka kawai yace su tafi Fika. "Uncle ina da imani zan iya daukar kaddara, ko mene ne kada ka boye min" muryarta na rawa tace "tsoro nake ji" Rungumeta yayi yana shafa mata baya. A nutse ya fada mata yadda sukayi da Harisu tace to Allah Yasa alkhairi a tafiyar. Kafin biyar sun dauki hanyar Fika a hanya suka dauki Amir da Mu'allim suka dawo motarsu saboda kada su Mama su takura. ***** Yau matan Harisu da mai girki da mara girki duka suna kitchen suna girki tare saboda bakin da suke kan hanya da su Gimbi. Dakuna aka gyara inda za'a saukesu. Awaisu ma da yake barin key din dakinsa shima an gyara masa nasa dakin. Sai shabiyu saura suka iso gidan. Lokacin su Daula duka sunyi bacci. A gajiye suke sosai musamman Awaisu da kanin Gimbi da sukayi tuki. Suna shigowa hayaniya ta kacame ana murnar ganin su Haris da amarya Rumana. Ita kuwa sam hankalinta bai kwanta ba sai da ta ga kowa na gidan lafiya. Daga dakin da su Gimbi suke suna jiyo muryoyin mutanen gidan da su Amir masu cigiyar Mummynsu. "Gimbi ba ke ake nema ba kuwa" cewar Haj. Fanta tana kallon kofa. Murmushi mai ciwo tayi "Hajiya bana son yaran nan su ganni sai na tabbatar su Maamu sun yafe min. Wallahi ba don dare ba ni a yau naso a zauna muyi magana na roki gafara. A haka ji n nake kamar akan kaya" Dr. Yana ta dafa kafadarta tana murmushi "kada ki damu don bana jin a yadda naga mutanen gidan nan zasu watsa miki kasa a ido. Ga dukkan alamu suna da kirki sosai" "Kirkin nasu shi yasa nake kara tsanar kaina da abubuwan da nayi musu. Gara ka cuci mugu akan mai kirki doctor " Daga bangaren su Baaba kuwa sun yiwa baki su Alh Mudi da Mama tarba da mutumci aka kaisu masaukin da aka tanadar musu. Yaran kuma tuni suka shige wurin 'yan uwansu bacci ya gudu. Abinci suka ci kawai suka shiga hayaniya a gidan. Anti Amarya ta kira Rumana ta bata key din dakin Awaisu "Ga mukullinku nan har abincinku an ajiye a ciki" Baki ta turo "to bari na kai masa na dauko kayana" "Kada ma ki bari babanku yaji wallahi ki wuce bakinki alaikum ki tafi dakin mijinki ni babu ruwana" Tafiyarta tayi ta bar Rumana saroro tana jin kunya ga su Maamu a wurin da mamanta. Antin ma tana sane tayi mata haka don ta kula da take takenta tunda suka shigo wurin 'yan uwanta take neman shigewa ta kwana. A falo Awaisu ne da Harisu da kuma Mujahid. Sun tambayeshi dalilin zuwan yayi murmushi yace su yi hakuri har zuwa wayewar gari tunda yanzu dare yayi. Ya dai kwantar musu da hankali cewa alkhairi ne ya kawosu. Ba don Rumana taso ba Baaba da kanta ta korata dakin Awaisu tana cewa bata son sakarci. Bai nemi Gimbi ba dama saboda ganin dare yayi kuma yasan taji zuwansu. Tunda bata fito ba zai hakura zuwa safiyar kamar kowa. Da ya shiga daki can karshen kujera ya tarar da Rumana a zaune ta takure. Tunda ta shigo tayi wanka take zaune a wuri daya. Yanzu ace duka gidan sun san tana dakin Uncle Awaisu ai da kunya. Murmushi yayi don kuwa yana jinta ita da Baaba Hure lokacin da tace mata dole ta tafi wurin mijinta. Kin kulata yayi ya shige bandaki yayi wanka ya fito. Tana nan zaune ya gama shirinsa duka baice mata komai ba ya kashe fitilar dakin ya kwanta. Sheshshekar kukanta yaji yayi 'yar dariya. A dan zamansu ya kula babu abinda Rumanansa taki jini kamar a shareta. Yana daga kwance yace "waye nan" "Shine ma kaki kulani" ta fashe masa da kuka bilhakki ita bata ji dadi ba. A duhun ya taso ya ja hannunta "nima fa kin kulani kika yi, ashe babu dadi. Kuma ina ji sai da aka tilasta miki zuwa nan saboda baki damu dani ba" Cike da shagwaba tace "na damu mana.." "Ban ga alama ba" Rungume shi tayi duk da tana jin kunya sosai "gashi kuwa..ni dama kunya nake ji yadda zan fita daga dakin nan gobe" Matseta yayi a jikinsa sosai "Sarkin rigima nima ai kunyar nake ji, kada ki damu na kusa gama gini a nan mu koma can duk lokacin da muka zo ko" Dariya yaji tana yi masa saboda yace yana jin kunya ya girgiza kai yana murmushi daga karshe ya sata yi masa tausa a kafa don ba karamar gajiya yayi ba. ***** Karfe tara na safe duk wanda ya kamata yazo yana cikin falon Harisu. Su Anti Baraka, matan Harisu, Maamu da Baaba, iyayen Gimbi, Dr. Yana, mijinta dasu Haj Fanta sai kuma Rumana wadda Maamu tace ko me za'ayi ayi a gabanta tunda dai matar Awaisu ce. Duk sun zauna suna sauraron Gimbi ta taso da idanunta kumburarru ta tafi gaban Maamu ta durkusa. Bude baki tayi zata fara magana sai kuka. Da kyar ta iya hada kalmomin Maamu ki yafe min. Kowa a wurin banda su Haj Fanta yayi mamaki. Maman Gimbi kuwa sai kuka a ranta tana cewa Alhamdulillah yau sun ga sakamakon jajircewa wurin yi mata addua. Maamu kanta hawaye ta soma yi "Gimbiya me ya sameki haka? Ko wani salon sihirin ne kika zo dashi?" Girgiza kai ta rinka yi sannan cikin kuka da tun jiya ta kasa dainawa ta labarta musu komai tun tsoron kada Maamu ta rabata da mijinta zuwa Anti Bebi da kuma wannan zuwan nata Damaturu. "Wallahi nasan bani da wani uzuri akan abubuwan da na aikata amma ina rokonku ku daure ku yafe min kada na mutu da hakkinku. Maamu ke nafi cuta shiyasa na damu nasan idan kika yafe min kowa a nan zaifi saurin hakura" Haj Fanta ita ta karbe ta basu labarin zuwansu Maiduguri a jiya da yadda suka kare da Malam sannan ita da su Yakura suka cigaba da nemarwa Gimbi afuwar wadanda ta sabawa. Tuni falon ya kaure da kabbara. Awaisu ya kasa cewa komai sai kallonta da yake yi amma baka iya tantance me zuciyarsa take tunani. Gimbi ta rike kafar Maamu "ki yafe min Maamu, mata irina da yawa suna cikin halaka. Wannan duniyar da bata da tabbas mun dauketa kamar bazata kare ba muna sabon Allah. Ina rokonku duka kuyi hakuri ku yafeni" A hankali Maamu ta dora hannunta akan Gimbi "Allah Ya yafe mana baki daya na yafe miki" Jikinta Gimbi ta fada tana kuka sosai. Dama can ita ba jahila bace son zuciya ne kawai ya kaita ya baro. Wurin da iyayenta suke zaune ta rarrafa suma ta basu hakuri. Maamu ma ta yafe bare su da suka haifeta. Haka ta rungume Mama tana kuka Alh Mudi yana mata addua. Daga nan shi da sauran manyan da suke wurin suka shiga yiwa kowa nasiha mai ratsa zuciya akan shirka da mu'amala da sihiri don neman biyan bukata. Allah SWT Shi kadai Ya cancanci a bauta Masa kuma a nemi taimako a gareshi domin Shine Ya haliccemu. Kusan awa daya ana ta magana daya sannan da daidai kowa ya fita harda Rumana aka bar Awaisu da Gimbi. Kasa kallonsa tayi da dukar da danta yana kallon hawayenta suna diga akan mayafinta. Tashi yayi tsaye a sanyaye yace "We used to be best friends Gimbi...what happened to us?" Sai lokacin ta dan dago kanta itama ta mike "son zuciyata ne ya faru Abban Haris, yau Maamu ko cewa tayi ka sakeni tun zuwanta gidanmu bai halatta na kaita wurin boka ba balle bata yi min komai ba. Ka yafe min mijina, ka taimakeni kada na nesanta daga rahamar mai rahama saboda wannan gagarumin sabon da na aikata" Idanunsa ya rufe sai ga hawaye suna sakko masa baiyi yunkurin tsayar dasu ko sharewa ba. Hannunta tasa a hankali tana share masa itama yana share nata. "Ban kyauta mana ba" "Kaddara ce" "Baka ce ka yafe min ba" "Addu'ata Allah Yasa muna da rabon sake zama a matsayin ma'aurata a lahira" Wata nannauyar ajiyar zuciya ta saki ta rungume shi tana kuka sosai. "I love you Abban Haris" Bai iya bata amsa ba sai bayanta da yake shafawa. Dago kanta tayi tayi masa murmushi "uwa ba abar wasa bace kuma nayi imani indai muna raye bazaka taba mantawa da yanayin da ka tsinci Maamu ba lokacin da ka dawo daidai duk lokacin da ka ganni. *Awaisu!* nasan duk duniya bani da masoyi kamarka amma da bakina ina rokonka ka sauwake min domin zamanmu bazai taba yiwuwa ba. Daga ranar da na fara kai kafata gidan boka na bata rayuwar aurenmu" Hannunsa ya dora akan bakinta yana girgiza mata kai ita kuwa ta zame shi tace ya barta ta fadi gaskiya. Ta tabbatar soyayya dai ta gaske yanzu Rumana yake yiwa kuma bata bakinciki. Fatanta ya sami nutsuwar da ta hanashi da soyayya ta gaskiya. A nasa bangaren ya yafe mata dama kullum fatansa ta gane gaskiya sai dai kamar yadda ta fada bazai taba mantawa ba. Maamu ita ce jigon rayuwarsa ta yaya za'ayi ya manta da hawayenta saboda soyayya. Wata takarda ya dauko daga aljihunsa wadda ya rubuta tun ranar da taje asibiti da wannan izgar dokin ya rubuta. Niyarsa sai ya hadata da limamin nan sannan ya bata. Hannu na rawa ta karba ta bude. Saki daya ne yayi mata idan aka hada da na baya ya zama biyu. Kuka ta saka duk da a ganinta ma yayi mata adalci da bai kai biyu ba ya raba tsakaninsu gabadaya. "Abban Haris nagode, lallai yau hannu ya girbe abinda ya shuka." Hakika Allah Yayi gaskiya da Yace *_la'in shakartum la aziddanahum wala in kafartum inna azabiy la shadid_*. Yau ga Gimbi da Allah SWT Ya ni'imta da abubuwa marasa kirguwa ciki harda miji nagari da suruka abar kwatance sai gashi haka nan babu gaira babu dalili ta janyowa kanta nesanta daga dukkan jindadin rayuwarta. "Allah mai gafara ne kisa wannan a ranki. All the best....my best friend. Ina miki fatan alkhairi a rayuwarki ta gaba" "Kaima Allah Ya baku zaman lafiya da Rumana" Share hawayenta tayi ta fito tsakar gidan tana kwalawa su Haris kira. Dama sun tashi suka fito a guje suna murnar ganinta. Dakin da aka sauki su Mama ta wuce tare da yaran ta basu takardar sakin. Sun gama hada kayansu tsaf suka fito nan kowa ya san hukuncin da Awaisu ya yanke tsakaninsa da Gimbi. Sai da taje dakin kowa ta musu sallama sannan ta roki a barsu su tafi da yaranta tayi kewarsu sosai. Baaba Hure tace ai babu mai hanawa. A mutumce suka yi sallama Gimbi ta rungume Haj Fanta tana kuka "Ki bar kuka Gimbiya inda rai da rabo kinji" Murmushi Gimbi tayi "ina kika baro Gombo kuma Hajiya?" "Tun jiya na nemeta na rasa sai Gimbiya uwar Harisu nake gani" Dariya aka rinka yi da alkawarin zumunci sannan Mujahid yaja motarsa shima kanin Gimbi yaja tasu motar suka kama hanyar Abuja. Rumana da Awaisu sai washegari suka tafi da sassafe don baya son ta sake fashin makaranta. ****** *Bayan Sati Hudu* Rumana ta gama girkin dare Daula kuma ta wanke duk abinda suka bata wurin girkin Haris ne mai jere kwanukan akan dinning table suna ta surutunsu. Bayan sun gama Rumana ta zubawa kowa sannan ta tafi tayi wanka kafin Awaisu ya shigo. Shiru bata fato ba suka gama ci suna kallon cartoon har Awaisu ya dawo. Da murna suka tare shi suna bashi labarin zuwansu gidan Mama yau da sakon Gimbi na gaisuwa gareshi. "To ina amsawa bari naje nayi wanka na fito. Inna Ammin ku?" Mu'allim yace itama wanka taje tayi. Dakinta ya fara zuwa bata nan sai ya wuce nasa dakin. A kwance ya ganta ta rufa da bargo tana bacci. Kasa shiga wankan yayi sai da yayi kissing dinta ya wuce yana tunanin neman mai aiki. Ga karatu ga aikin gida yasan abin yana mata yawa. Har ya fito tana nan kwance ya gama shirinsa ya kula tana yamutsa fuska cikin baccin sai ya zauna a gefen gadon ya dora hannunsa akan goshinta zai shafa yaga tayi mugun zabura amma bata bude idon ba "Don Allah Anti kiyi hakuri" Abinda yaji tana fada kenan sai ga hawaye ta soma kamar famfo. Jijjigata ya somayi a rude taki tashi sai kiran Anti da take yi tana kuka. Rasa abinyi yayi kawai ya bude quilt din da ta rufa ya dagota sai kawai jikinta ya saki jini ya balle mata cikin dan kankanin lokaci ya soma bin gadon. Firgici da tsoro kan Awaisu ya gama yi. A guje ya dauko jallabiyarsa ya dora mata akan rigar baccin jikinta ya dauketa yayi falo. Yaran duka suka taso yace musu bata da lafiya su kula da gidan zai turo azo a daukesu baya son su zauna su kadai. Duka sun tsorata ganin Ammi kamar yadda suke kiranta bata ko motsi. Gudu sosai yake yi ya karasa national hospital saboda yana tsoron zuwa private ace babu likita. Sake daukarta yayi ya shigarda ita emergency nan suka karbeta aka fara bata taimakon gaggawa. Awaisu yana reception ya dai kira Nuru ya fada masa yaje ya dauki su Haris. Shiru likitocin basu fito ba daga dakin da take har Nuru ya kaisu gidansa ya taho shima. Ledar jini uku aka karawa Rumana. Tashin hankali karshe Awaisu ya gani a wannan daren. Da suka fito ne suka yi masa bayani cewa bari tayi ya kuma fita duka amma ba shi bane ya daga musu hankali kamar jinin da take zubarwa. Sai dai suna ganin sun shawo kan matsalar yanzu in sha Allah. Yadda baisan da cikin ba ya tabbatar da wuya idan Rumanan ma ta sani. Tausayinta yaji ya kamashi ya tafi gida dauko mata kaya da shirin kwanciya. Amenity ya biya Nuru yace zai turo Kubra ta kwana Awaisu yace ya gode amma shi zai kwana da ita. Shabiyun dare ya dawo asibitin har lokacin bata farka ba. Likita dai ya tabbatar masa da cewa bata cikin hatsari yanzu bacci ne kawai take yi saboda allurai da akayi mata. A zaune ya kwana a gefen gadon. Sai wurin takwas na safe ta farka tana rike ciki. Kanta ne ya nemi juyewa bata gane ina suke ba. "Son So..." Da sauri ya taso daga kan kujerar yazo ya duka inda take kwance ya rungumeta yana ajiyar zuciya. "Sannu kinji" "Me muke yi a nan?" Gabansa ne ya fadi "baki da lafiya ne na kawoki jiya. Ina zuwa zan fadawa dr kin tashi" Hannunsa yaji ta rike "me ya sameni?" Bai iya bata amsa ba ya fita can sai gasu sun dawo da likita. Dubata yayi ya gama rubuce rubucensa ya fita. Taimaka mata yayi ta zauna ta sake tambayarsa me ya kawota asibiti. "We lost our baby Umm Ruman" Zaro ido tayi tare da dora hannu akan cikinta "dama...dama...ina da...?" Sai kuka kuma. "Shhhh kada ki damu muyi fatan shine alkhairinmu kinji ko. Allah zai kawo mana wasu masu albarka" A hankali ta gyada kanta ya rungumeta yana rarrashinta. Suna zaune a haka ya kira Harisu ya fada masa. Nan da nan duka gidan suka sani. Maman Rumana ta shiga damuwa sosai har Baaba ta kula da hakan ta fadawa Harisu gobe idan zasu tafi lallai a tafi da ita ta ga 'yarta. Yinin ranar Awaisu baya fita daga dakin sai sallah. Daga gidan Nuru aka rinka kawo musu abinci. Washegari da yamma su Maamu suka iso. Kafin su wuce asibitin da kanta ta yiwa Rumana girki. Miya ce ta ganyen alayyahu, ugu, shuwaka wadda taji wanki sosai babu daci sai zogale ga hanta, bushasshen kifi da koda anyita da manja. Kana ganin miyar kasan girkin ya sami kulawa daga maiyi. Tuwon semo ta tuka mai kyau da ya dahu taje yin wanka Maman Rumana ce ta kulle a leda suka shirya suka tafi. Abin nema ya samu tana ganin iyayenta da Maamu sai shagwaba ta karu. Abincin ma cewa tayi bazata iya ci ba Maamu kuwa tace Awaisu ya zauna ya bata. Kunya kamar ya nutse ganin idonsu Harisu. Maamu ta soma fada idan bazai tashi bane ita sai tayi. Yana mikewa kuwa Mama da Harisu suka kusa karo suna neman hanyar ficewa daga dakin suma kunyar suke ji. Rumana da ta janyo abin daskarewa tayi a zaune tana takaicin me ya hanata ci da kanta. Maamu ta kallesu duka tace "gulmammu". Nuru da Kubra me zasuyi in na dariya ba. Bayan kwana uku aka sallameta su Harisu suka koma Fika. A satin Awaisu yace a nemo masa 'yar aiki aka samo wata mata zatayi kusan shekara arba'in Hanne. Ita take kula da shara da goge gogen gidan banda dakin Rumana da Awaisu. Sai taimakawa wajen girki da kula da yara. Zamansu suke cikin farinciki da kwanciyar hankali. Wata biyu a tsakani Rumana ta sake samun ciki. Wannan karon ma basu sani ba saboda baifi sati hudu ba. Tana wanka Awaisu yana aiki a dakin yaji kamar ta fadi. Bai san lokacin da ya ture laptop din ba ya tashi da sauri ya bude kofar. A kwance ya sameta gefen baho ga jini yana bin kafafunta. Tsoro sosai yaji ya dagota da sauri yana kiranta. Shiru kamar wancan lokacin sai Anti da take kira cikin galabaitacciyar murya. Wannan karon banda fargaba harda mugun bacin rai. Wancan lokacin baya son saka zargi a ransa amma yanzu tabbas abin ya zauna masa a rai. Maamu ce tayi zaman jinyarta don sai da aka hada da wankin ciki. Tasha wahala sosai akayi sa'a cikin sati daya ta sami sauki. Haka rayuwa taci gaba Awaisu na kula da iyalinsa sosai sai dai ya kasa cire abubuwan da suka sami Rumana. Ko da ya tambayeta me take gani kafin tayi barin cewa tayi bata iya tuna komai. Karo na uku da ta sake yin barin kiransa akayi yana wurin aiki yazo makarantarsu. Kafin yaje sun kaita asibiti saboda irin jinin da take zubarwa. Tana zaune a aji kawai ta kwantar da kanta kamar mai bacci wadda ke zaune a bayanta ce ta sanar da malamar dake ajin tana bleeding. Da yake basu san tana da aure ba duk anyi zaton wata matsalar ke damunta. Awaisu bai bata lokaci ba ya isa asibitin abinda yaji tsoro ne wato ta sake yin bari. Jikinsa har wani tsuma yake yi yana tabbatarwa ta sami kulawa ga Maamu a kusa ya tafi gidan Alh Mudi. ****** Cikin girmamawa ya gaishe da Mama yace yana neman Gimbi. Tana daki da yake yanzu can tafi zama tana karatu saboda masters da ta koma Mama tace Awaisu yana kiranta. Karamin hijabi ta saka ta fito falon. Ko zama batayi ba Awaisu ya tareta cikin bacin rai "Gimbi me nayi miki haka da zafi ne?" Kallon rashin fahimta tayi masa ita kuwa Mama jin ya daga murya ta kasa karasa barin wurin ta tsaya daga bakin kofar falon "Bangane ba?" "To bari nayi miki kashedi gwaro gwari. Wannan ya zama karo na karshe da zaki zubarwa da Rumana ciki. Na rantse miki idan irin haka ya sake faruwa zan kawar da duk wani sauran mutumcin da yake tsakaninmu na dauki mataki" Kirjinta ta dafe da yake neman bugawa saboda ciwon da yake yi mata. Wannan mugun son da take yiwa Awaisu har yanzu da tuni ta gama iddah bai barta ba sai ma abinda ya karu. Hawaye ta soma yi "Abban Haris wani ne yace maka na zubar mata da ciki?" Yatsunsa uku ya daga a gabanta "sau uku kenan Rumana tana bari. Ko yaushe idan abin zai faru sai dai ta kwanta kamar mai bacci tayi ta ambaton sunanki daga nan bazata sake farkawa da cikin ba. Na dauke kai iya yadda zan iya amma bazan zuba ido ki nakasa min mata ba" A fusace ya fita tana kiransa ko waige babu. Ta juya ta koma daki taji saukar maruka masu radadi har uku a kuncinta. Mama ce tsaye tana hawaye tana hucin bakinciki "Gimbi ashe tuban muzuru kika yi mana dama? Zubar da ciki har sau uku don rashin imani. Irin haka fa kika yiwa Dr. Yana gashi ita har yau shiru kake ji " Gimbi na kuka take ta rantsuwar ba ita bace amma a banza. Alh Mudi Mama take jira ya dawo ta fada masa. Da ta koma daki Dr. Yana ta kira ta tambayeta yanayin da ta shiga lokacin da tayi bari. Ta kasa fahimtar dalilin tambayar gashi Gimbin kuka take yi ta fada mata. Tana ji hankali a tashe ta dauki mukullin motar da take amfani da ita a gidan ta tafi gidan su Ovi. Ita ce kuwa ta bude kofar tana mata murmushi "gaskiya Awaisun nan naki yana da hakuri indai sai yanzu kika sami sakona" "Me kike nufi Ovi?" "Ina nufin duka zubewar cikin matarsa bai taba nuna yasan kece ba sai na yau ko." Dariya take yi ta shige ta bawa Gimbi hanya ta shiga cikin gidan. Ovi da kanta ta fadawa Gimbi ita ke sawa boka ya zubar da cikin Rumana kuma ya tabbatar yayi yadda za'a zargi Gimbi. "Mijinki ya bata min rayuwa duk iskancina ban taba kwana a cell ba sai dalilinku ke da shi. Ki dauka ramuwa ce kawai nayi amma bana jin zan taba bari ta haihu yadda kanwata bata shiga ba ita bari zata rinka yi mai ciwo ke kuma ayi ta zarginki" Mari Gimbi ta sharara mata ta dafe kunci tace ta kiyaye abinda zai biyo bayanta. Fada sosai suka yi na cacar baki sannan Gimbi tazo fita tayi saurin jiyawa gefen kujera inda ta hango wata bakar tukunyar kasa. Dama tasan bokan Ovi ayyukansa yawanci da tukunyar tsafi ne tuni zuciyarta ta bata dashi ake tsafin zubar da cikin. A guje ta ruga ta daga tukunyar Ovi tana ihu ta rotsata da kasa. Kanta Ovi tayo ta fita da gudu ko takalmi bata saka ba Ovi na bayanta ta hankadata kasan benen gidansu dama a sama suke. Duk abinda suke yi Rita tana daki tana jinsu kawai bata son shiga ne. Gudun da taji ne yasa ta fito daidai lokacin da Ovi ta hankada Gimbi. Duka sun rikice Ovi ta gudu daga gidan ita kuma Rita wayarta ta laluba ta kira Awaisu dama tana da numbarsa. Yana tsaye gaban Rumana yana jin kamar yayi kuka sai ga Mama ta shigo tana share hawaye tana basu hakuri. Ko da Rita ta kira kamar kada ya daga sai kuma ya daure yasa wayar a kunne. Don kada ya ajiye yaki sauraronta fada masa Gimbi na gidansu ta farayi sannan tayi masa bayanin komai. Bai iya magana ba sai salati ya sake kwasa sai gidansu Ovi yana bin kwatancen Rita. A kasa ya sami Gimbi bata motsi shima da hawaye baya masa wuya sai gashi sun zubo. A bayan mota ya sakata Rita tabi bayansa a taxi. Emergency aka kaita suka duba ta sannan aka bata gado kusa da na Rumana. Rita gwiwa a kasa ta rokesu gafara sannan ta fada musu duk abinda Ovi tayi. Mama na rungume da Gimbi tana kuka Rumana ta farka. Lokacin Awaisu ya kira abokinsa DPO ya fada masa duk inda Ovi take su kamata. Sai gashi Rumana ta tashi amma Gimbi sai yamma ta farfado. Likitan da ya dubata yace ta sami sauki buguwa ce dama da karaya a hannu wadda suka gyara. Waahegari haka su Awaisu suka sake biyo hanya shima Alh Saminun Kano yazo duka suka hado a asibitin ana yiwa juna jaje. Shuhada da iyayenta ma duka sunje. Rumana bacci take yi lokacin likita yazo dubasu kowa ya fita. Wurin Gimbi doctor din ta tsaya "Yanzu bazaki yarda na fadawa 'yan uwanki ainihin ciwon da yake damunki ba?" Gimbi ta girgiza kai tana hawaye "ko kin fada bashi da magani. Na rasa wace irin soyayya ce nake yiwa tsohon mijina" "Har fa aman jini kike yi, ki bari a taimaka miki" doctor ta fada tana tausasa murya. "Kada ki dami kanki ina bakin kokarina wurin cire sonshi daga zuciyata. Akwai kunya mai girma idan nace zan zauna dashi. Labarin darasi ne ga mata. Ke dai duk yadda zakiyi a rayuwa ki tabbatar baki cuci kowa ba, mafi alkhairi gareki shine a cuceki Allah sai Ya isar miki" Hawaye ne ya gangarowa Rumana amma tayi dif kamar bacci take yi. Zantuka masu ban tausayi Gimbi take yi a take taji mugun tausayinta kuma ta kara sonta domin taji komai game da yadda ta fasa abinda akayi mata tsafi dashi. Da daddare Rumana ta kafe babanta Harisu da ido idan zai juyo sau biyar sai sun hada ido. Hawaye ya gani fal idon sai yaji tace ya kaita waje tasha iska. Awaisu da bai san ta tashi ba ya taso da sauri sai dai Harisu ya fuskanci bakinta da magana yace masa bari ya fita da ita shima kafarsa tayi tsami. Basu kawo komai ba ya rike hannunta tana tafiya da kyar. Waje suka fita ya zaunar da ita kan wani benci sannan ya zauna a gefe yana rike da hannunta "Umm Ruman me kike son sanar da mahaifinki?" Sunanta kawai da ya ambata ya karyar mata zuciya ta soma kuka. A haka ta fada masa abinda taji. Shima maganar ta tsaya masa a rai Cike da kulawa yake mata magana "yanzu me kike so?" Kai ta sunkuyar "Baba don Allah a mayar da aurenta da Son Son...auuuu" ta toshe bakinta da sauri tana dariya. Shima dariyar yayi "kaniyarki wato Awaisu ya sa kinyi fatali da kunya ko" hannunta ya kama ta tashi. "Allah Yayi miki albarka Rumana Harisu lallai na yarda da yardar Allah ku ma zaku zama mutane masu sadaukarwa domin farantawa 'yan uwa musulmi. Ina alfahari dake domin kin kasance mai hakuri da biyayya. Muje ciki" Dakin suka koma kowa na ciki suna shirin fita ne ma. Alh Saminu, Alh Mudi, Nuru, Alh Maitama sai Awaisu. Abin mamaki Baaba Hure ke bawa Gimbi abinci a baki saboda karayarta ga Mamanta a gefe baki har kunne yadda take yaba kirkin wadannan mutane. Harisu ya nemi ganin mazan suka fito duka. Yadda sukayi da Rumana ya fada musu Alh Mudi hankalinsa ya tashi jin cewa Gimbi na da matsalar zuciya. Awaisu ma ba karamin rudewa yayi ba. Harisu ya dafa kafadarsa "tashin hankali ba namu bane tunda munsan matsalarta. Shawarata kamar yadda mukayi da Rumana shine Alhaji ka wakilta wani cikinmu ya zama waliyyin Gimbi a maida aurenta da Awaisu tunda akwai sauran igiya daya tsakaninsu." Da sauri Alh Mudi ya girgiza kai "inaaa, bana marmarin a sake komawa gidan jiya. Gimbi bata kyauta muku ba Harisu" "Ashe bamu yafe mata ba kenan tunda har yanzu muna tsoronta bazamu iya zama da ita da zuciya daya ba." Cewar Harisu Awaisu bai iya magana ba sai mamakin Rumana da har ta san ta sowa wani abinda take so. Yana ji suna ta maganganu sai daga karshe yace musu shi dai ya amince a mayar da aurensa da Gimbi. Batare da bata lokaci ba Alh Maitama ya yiwa Gimbi waliyyi shi kuma Harisu ya nemi auren Gimbi ga kaninsa a wurinsa. Basu koma ciki ba sai da aka damkawa Alh mudi sadakin yarsa a hannunsa. Har kuka yayi saboda farinciki yana ta yi musu godiya. Dakin suka koma akace duk su fito su tafi gida. Mama taso sake kwana da Gimbi Alh Mudi yace tazo su tafi yana da magana da ita. Ya rage dakin daga Awaisu sai matansa. Gadon Rumana ya fara zuwa yana murmushi ya rike hannunta "Sweet Son So naji duk abinda kika yi bansan da me zan gode miki ko saka miki ba. I simply love you" Gimbi tana jinsu hawaye ya zubo mata ta share tana murmushi "ehemm ehemm da mutum dai a kusa" Awaisu yayi dariya "kinsan uwargida a ko ina ita ce gaba sai na sallameta zan zo wurinki" Rumana taji gabanta yayi mugun faduwa ta matse hannun Awaisu. Kallon cikin ido yayi mata "Kada ki karaya kinsan bazan taba wulakanta ki ba" hannunsa ya hade yayi mata alamar yana sonta yadda suke yawan yiwa juna sannan ya juya ya fuskanci Gimbi. Da sauri Rumana ta fice daga dakin tayi sa'a iyayenta da Maamu da Baaba ashe basu tafi ba. Jikin Maamu ta fada tana kuka duk suna bata hakuri Harisu ya sanar da su abinda tayi. A cikin dakin kuma Awaisu bakin gadon Gimbi yaje duk da yaji kamar ya bi bayan Rumana. "Amaryar Abban Haris yaya naki jikin?" "Me kace?" "Ina nufin dazun nan aka mayar da aurenmu da Gimbiyata" Wani kuka ne ya taso mata ta rungume shi tana yi yana bata hakuri "Rumana ce ko? Ashe zan sake amsa sunan matar aure kafin..." Bakinsa ya hada da nata ya shiga kissing taji kamar yau ta fara ganin Awaisu yau ta fara sonsa. "Abinda kuka yi min Allah Ya saka muku da alkhairi nagode. Allah Ya baku zaman lafiya da Rumana. Da zan sake haihuwa sai nayi mata takwara saboda tayi min halacci. Ta bani abinda ban taba zaton sake samu ba. Rumana ta hadani da farinciki mara misaltuwa. I love you so much" Rumana dagewa tayi a sallameta a ranar dole suka bari ta tafi. Ita kuwa tayi haka ne saboda ta bar Awaisu da Gimbi su kadai. Da suka koma gida su Baaba sai tarairayarta suke yi. Awaisu kansa sai waya yake yawan yi mata a karo na hudu da ya kira ta kashe wayar. Washegari su Dr. Yana suka zo sai ga su Anti Baraka. Gida ya cika da mutane haka asibitin. Anyi nasarar kamo Ovi Awaisu yaje police station din ba don an rike shi ba yadda ya fara kwallo da ita da itama a asibitin zata kare. Yana dawowa ya samesu a waje aka ce masa jikin Gimbi yayi tsanani. A firgice ya shiga dakin doctor zai salleme shi Gimbi a wahale ta hana. Gaban gadon yaje ya durkusa ya rike hannunta. Nan likitan yace zuciyarta a kumbure take za'ayi mata gwaje gwaje yace ya amince ko me zasuyi ayi mata. Fita yayi kiran masu daukarta a kaita dakin gwajin. Awaisu ya shafi fuskarta "Me yasa kika boye mana rashin lafiyarki?" Murmushi tayi cikin jin ciwo "gashi yanzu ya fito har ka kawo mij sauki" "Nagode da dukkan soyayyarki gareni Gimbiya. I love you so much" Kai ta kada a hankali "Abban Haris ka dade baka kirani da sunana ba" Kanta ya dora a kafadarsa suna zaune kusa da juna hannunsu sarke " _Nana Fadima_my best friend" Ajiyar zuciya tayi sai yaji muryarta ta kara yin kasa tana ambaton Allah a hankali. Bayan kamar minti biyu yaji shiru sai sassautawa rikon da tayi kasa. A razane ya dagata " *Gimbi!!!!*" Kan kace me dakin ya cika Baaba Hure ta janyeta daga jikin Awaisu ta kwantar tare da rufe mata ido. Hakan yayi daidai da bugawar zuciyarsa ya sulale a kasa shima. "Innalillahi wa inna ilaihi rajiun...Allah Ya jikanki Gimbiya" cewar Alh Mudi Kuka ne ya kaure a dakin doctor na dawowa ya tabbatar musu ta rasu sannan aka bawa Awaisu taimakon da ya dace. Sun ga tashin hankali Rumana ta rinka kuka ta tsorata da mutuwa. Ga su Daula da Awaisu abin tausayi. Kafin azahar an kaita makwancinta suna ta yabon yadda karshenta yayi kyau ana dada yafe mata. Kamar daga sama Anti Bebi ta shigo gidan ta fada jikin Mama. "Yaya Amina ki yafe min ni na sawa Gimbiya ciwon zuciya saboda muguwar soyayyar da aka dasa mata na Awaisu. Gimbiya ta tafi ta barni a wannan duniyar abar banza ko gafararta ban roka ba na cutar muku da 'ya saboda keta" Mama ta dago jajayen idanu "wadda kika yiwa ma ta tafi me zai hana na yafe miki Bebi? Duniya ce dai ki kiyayeta don bata da alkawari" Zaman makokin kwana uku akayi sannan suka watse sai adduar Allah Ya jikan mamatanmu Ya bamu cikawa da kyau da imani. **** *Bayan Wata Shida* Rumana an gama SSCE ta dawo gida Awaisu ya shirya mata walima ta iya su mutan gidan. Taji dadi sosai suka wuni suna hayaniya da yara yadda suka saba. Da daddare sun kwanta yake fada mata an kawo kudin Shuhada bikinta saura wata biyu. "Ashe zamu girgiza jiki a wurin biki" Baki ya rike yana kallonta "ke! Wa zaki je ki girgizawa jikina?" Ta hau dariya dama tsokanarsa take yi tasan shi da kishi. To ma me zai kaita rawa gaban wasu da aurenta, yan mata ma ana musu nasihar su bari. "Dariya kike yi ko. Kin fasa zuwa bikin" Kafa ta soma bugawa "haba Son So nice fa" Ya kalleta a karkace "ban sanki ba" "Shuuuuhhhhh ...wayyo bakina naga boni" Daukota yayi ya dorata kan cinyarsa shima yana dariya "za dai ki ganshi yanzu, me ya sami bakin" "Ka bani magani indomie mai romo naci" "Ai ba sai kin roka ba" Sun dade yana kissing dinta sannan suka kwanta ta kamo hannunsa tana wasa dashi "Son So" "Yes kwailar Awaisu" "Na fasa yi maka albishir din ma" "Yi hakuri ni da na shaida mata ta tafi kwaila" Zumboro baki tayi ta tashi zaune tana shafa cikinta "little Gimbi kinji Abbanki yace min kwaila ko" Zama yayi sosai yana kallon cikin "are you serious?" Kunya taji ta kwantar da kanta a kirjinsa "jiya da nace maka zamu je asibiti da Amir yana mura harda kaina na kai. Kuma in sha Allah Nana Fadima Gimbiyar Uncle Awaisu da Umm Rumana zan haifa" "Amin Son So Amin" Bargo ya ja ya rufe su aka bude sabon shafin soyayya. *Alhamdulillah* Dukkan yabo da godiya ya tabbata ga Allah Madaukakin Sarki da Ya bani ikon farawa da gamawa lafiya. Abinda na rubuta daidai daga Allah ne ina rokonSa Ya bamu ikon aiki dashi. Wanda nayi kuskure daga gareni Allah Ya yafe min daku baki daya. *Sadaukarwa* Ga dukkan uwarmiji da suruka ta hanata zaman lafiya da danta. Allah Ya ganar da masu wannan hali su san cewa uwa ba abar wasa bace kuma soyayyarki ga miji shine kiso iyayensa. *Tukwici* Gareki Aisha Maman Abida. Nagode Allah Ya bar zumunci. *Gaisuwa da fatan alkhairi* Taurarin Fikra Writers Association Dukkunan matan BMN Batul Mamman grp ban dauke kowa ba. Allah Ya saka da alkhairi. Abin da yawa wallahi bazan iya jero sunaye ba amma kunsan kanku. Nagode da soyayyarku gareni. Zauren zumunci online Taskira Zauren Biebee Isa Maman Haneep novel Feenat Ja'afar novella ROF 1 and 2 Hausa Nvls only Futuhatul khair novels Aysha Garkuwa nvls RAZ novella Umm Subay'a fans *Bazan manta daku ba* Riri Turaki Zee Bells Murjanatu Alkali Meela Adeel Rally Garba Wasila (mmn haneep nvl) Mum Little Umm Nass Pherty Zahra