[1/18, 13:55] Maryam S Indabawa🥰: ASMA'U HUSNAH* BY *MARYAM S INDABAWA* *MANS* 🌐HAJOW📝🌐 👩‍👧‍👧👩‍👧‍👧👩‍👧‍👧 HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS✍🏾✍🏾✍🏾 *don't forget to follow and vote @ Msindabawa* Page *1-5* Da sunan Allah mai rahama da jin kai duk kan yabo ya tabbata ga Allah da kuma annabin sa Muhammad (SAW). Ina godiya da Allah da ya bani ikon kammala *Koma kan mashekiya* Ya bani damar fara wani sabon littafi *ASMA'U HUSNAH* To Alhamdulillah ina godiya ga rabbil samati wal ardi. Kuma ina rokan Allah ya bani ikon farawa lafiya tare da kammalawa lafiya *Ameen* Ya Allah ka jagorance ni wajen mika sakon da nake son mikawa. Allah ka shigen gaba. Allah ka sa mu gama lafiya. *Ameen!* Wannan labarin kagage ne, ni na kirkire shi in kag yayi dai dai da rayuwar ki/ka akasi aka samu. Da fatan zzai nishandar ya kuma fadakar da masu karatu. *Nagode* *Asma'u Husnah* littafinne da ya shafi soyayya, akwai abubuwan tausayi, da zalunci da yan matan suke da yawan yin sa nabin wajen malamai.* *Banyi alkawarin baku posting kullun ba amman in lokaci ya samu zaku samu da yaddar Allah.* Bari dai mu shiga daga ciki dan jin abinda ke ciki. *THE WHOLE BOOK* *DEDICATED TO MY LOVELLY MOMY* Allah ya kara miki lafiya da nisan kwana. Ameen Ya Allah. Kwance take akan gadon ta. Katone, dakin ma kasan abin kalla ne. Komai na ciki ruwan hoda ne. Gefen gadon durowa ce katuwa, sai mudubi, sai wani table dake gefe. Littafai ne a cike akai. Gefen dama littafan isilamiyya daya gefen kuma na boko. Sai wata sofa dake gefe guda. Sai wajen takalman ta, da jakun kuna, dakin sai kamshi yake ko ina a gyara tsab. Sanyin AC ya ratsa shi, ga dadadan kamshi. Gefe wata kofa ce guda biyu daya wacce zata sada ka da cikin gidan ce. Daya kuma ta bandakin ta ne. Idon ta a lumshe sai zuba murmushi take. Baka ce, amman bakin ta me kyau ne irin sune black beauty. tana da hanci da idanu, da yar haba, sai kumatun ta dake a lubawa sanadin murmushin da take. Girar ta cike take da gashi wanda yake a kwance ke kace gyara ta akayi ko zane akayi ma. Gashin kanta har gadon baya. Leben ta me kyau da taushi. Pink colour. Magana take kasa kasa cikin zagin muryar ta mai dadin sauraro wacce duk wandan ya saurare ta sai yaso kara saurara ta. Kunne na kasa dan jin me take cewa. Muryar ya me sanyi da zaki naji tana cewa, "Haba Yayana ai nima ka riga da ka dauken tawa zuciyar dan ban da wani abinda nake so da kauna da ya wuce kai." Fulon dake gefen ta, shi ta ja jikin ta, ta rumgume shi. Tana sauraron maganar da ake fadi daga can ban garen. Murmushi ta sake saki wanda ya har sai da hakoran ta farare masu kyau, wanda yake dauke da wushirya ya bayyana. Magana ta fara cikin shagwaba kamar zatayi kuka. "Wallahi, nima haka." Shiru ta kuma yi tana sauke ajiyar zuciya. Mikewa tayi daga kwancen da take, wayar ta cire a kunne tana sa ta a spearker. Gyara zama tayi, tana gyaran gashin kanta da ya barbaje a bayan ta. Murmushin fuskar ta be dauke ba. Muryar sa me dadi ta cikaken namiji ta fito ras sai kace a dakin yake. "Baby na kin fiya shagwaba fa. banda burin da ya wuce na ganmu tare a matsayin ma'aurata. Kece farinciki na. Dake nake son na rayu na kuma mutu dake." Murmushi da take yi ne ya nin ku. Dan na yanzu har da sauti. "Nima haka, na maka alkawarin bazan taba barin ka ba har sai in kai ka bukaci haka." Ta fada tana daure kanta da ribon. "Wayoo Allah baby nah! Tayaya zan bukaci rabuwa da rayuwa ta. ai Bazan iya ba." "Yayana ina son ka." "Baby na son da nake miki bazai taba misaltuwa ba." Ido ta lumshe lokacin da ya fara fado mata wasu dada dan kalamai. Ji tayi kamar duk duniya ba wanda yafita dace da masoyi, ba kuma wanda yake cikin farin cikin da take ciki. Ya dade yana sanyaya mata zuciyar ta da sata nishadi sannan sukai sallama badan sun so ba sai dan kiran magariba da sukaji ana yi. "Baby nah! je kiyi sallah!" "To Yayana." "Ayi mana addu'a" "Insha Allahu." Kiss ya blowing ta cikin wayar, wanda taji kamar a fili yayi dan yadda tsigar jikin ta ta tashi. Murmushi tayi, ta mike a hankali ta fada ban dakin dakin ta. Masha Allah ban dakin ma kasan sa abin kallo ne. Komai na ciki shima ruwan hoda ne. Wato pink colour. Wanka ta farayi sannan ta dauro alwala ta fito. Sai da ta goge jikin ta sannan ta dauki wata doguwar riga ta zuro ta dauki hijab ta, tada sallah. Tana idar wa ta jawo kur'anin ta, ta fara muraja'a sai da akayi isha'i sannan ta dire shi ta mike ta tada sallah. Ko da ta idar sai da tayi shafa'i da wuturi sannan ta dauko mannta cocoa butter, ta fara murje jikin ta dashi. Ko powder bata shafa ba, sai man lebe da ta murza akan tatausan leben ta. Riga da wando ta saka, rigar ta wuce gwiwar ta sai dogon wando. Turare ta bade jikin ta dashi sannan, ta nufi kofar da zata sada ta da cikin gidan. Katuwar barander ta fita. wacce take dauke da falo da aka saka mata kujeru masu kyau da tsari. Ko ina tsab dashi, sai tashin kamshi yake, ido ta lumshe sannan ta bude su. Tare da sakin murmushi. Matattakala ta nufa Wacce zata sada ta da babban falon gidan. Tana sauka, Murmushi dake kan fuskar ta ya fadada. ganin yan gidan nasu duk sun halarta a falon. Katon falo ne, da yasha kujeru masu kyau manya manya. Dakin sai tashin kamshi yake. Cikin tafiya me daukar hankali ta nufi wajen Dadyn ta. "Oyoyo Dady nah sannu da zuwa." Ta fada tana karasa wa wajen sa. Hannun ta ya kamo, "Oyoyo *Husnah* ya gidan?" Murmushin fuskar ta be bace ba, idon ta akan Mahaifin nata. Ta amsa masa da. "Lafiya lou Dady nah." Kallon ta yayi cikin kulawa, yace, "Makarantar fa. Ince ba matsala." Wani murmushi ta kuma sakar masa. "Dady komai lafiya Alhamdulillah." Shima murmushi yayi, yana kallon 'yar tasa, "Masha Allah! Allah kara dafawa." "Ameen ya Allah. Dady na taso kaci abinci kaji." Ta fada tana kamo Hannun sa. Yayan ta da ke gefe yayi tsaki ya mike ya kamo hannun Mamin su. Ya fara magana cikin kishi. "Mami na taso muje kici abinci." Dariya Dady yayi. Ya girgiza kan sa. *Asma'u* tace, "Wai dan na kula da Dady na ko?" "Ina ruwan ki badai Dady kika gani a falon ba kawai." Dariya tayi, Haka ma Dady har da Mami. "Haba Yayana sorry!" Ta fada da sigar tsokana, "Muje Dady na." Suka nufi daining gaba dayan su. Dady ta fara zubawa abincin sa, sannan ta hadawa Mami tana me murmushi. Ita da yayan ta, ta hada musu. "Yayana muci ko?" Hararar ta yayi ya dauki cokali, suka fara cin abincin. Sai da suka gama sannan ta kwashe kwanu kan tayi kitchen dasu ta wanke. A falo ta same su. Gefen Dady ta koma. "Dady Nah ya gajiyar aiki." "Gajiya babu." "Sannu toh! Allah kara budi da daukaka yasa ka gama lafiya ya jikan iyayen ka." "Ameen! Ameen! *Husnah tah.* " "Mami sannu da hutawa." Ta fada tana daga gefen Dadyn ta. "Sai da kika gama da Dadyn naki." Dady dariya yayi. "To kar ta kula da nine. Wai duk kishi kuke da ni bayan kunsan yadda nake da *Husnah* " "A'ah Dadyn *Asma'u* ni bance ba." Dariya ya kuma yi. "Naji baku fada ba amman kun nuna a fuskar ku ko?" *Asma'u* ce ta fara magana cikin shagwaba, "Uhmm Dadyn in fa baka nan dasu nake kula." "To yanzu na dawo kuma sai a kula dani ko?" "Eh man Dady nah." Ta fada tana dariya. Dariya sukai duka suka cigaba da hirar su. Tara da kwata *Asma'u* ta mike. "Dady nah sai da safe," "Allah tashe mu lafiya." Ya sumbace goshin ta murmushi ta sakar masa. Sannan ta wuce gun Mami. "Mami nah sai da safe." "Allah kaimu." "Ameen Mami nah." itama a kumatu ta sumbace ta. Murmushi tayi mata ta wuce gun Yayan ta. "Yayanah!" Banza yayi mata. "Haba Yaya nah." Hararar ta yayi "Shikenan. Yayana sai da safe." Ta shagwabe fuska tayi gaba. Janyo ta yayi, ta fado jikin sa. "Haba *Asmy nah* " Fuska ta hade idon ta na kawo ruwa. "A'ah dan Allah, kada kiyi. yi hakuri. Please Baby Asmy." Dariya ta saki tai masa gwalo ta mike daga kan cinyar sa. "Sai na fada wa Anty Zee nah." Ido ya zaro dan bai son su Mami suji. Yatsan sa ya daura akan leben sa. "Dan Allah man," Murmushi tayi. tana kada kai, Tayi hanyar benen. "Yayana Swt dreams of Ur Zee." Ta fada da karfi, ido ya zaro. Ya mike ya bita a guje. "Wayoo Dady night!" Ta diba a guje tayi daki ta rufe kofar ta. "Wallahi zan kamaki ne." "Naji din" Mami da Dady kuwa dariya suke dan *Asma'u* indai batai tsokana ba bata jin dadi indai tana waje sai anyi dariya. *don't forget to follow and vote @ Msindabawa* *Muje Zuwa.* *INDABAWA* [1/18, 13:55] Maryam S Indabawa🥰: *ASMA'U HUSNAH* BY *MARYAM S INDABAWA* *MANS* 🌐HAJOW📝🌐 👩‍👧‍👧👩‍👧‍👧👩‍👧‍👧 HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS✍🏾✍🏾✍🏾 Page *6-10* *Ummu nah* Abar alfahari na ina son ki da yawa Allah bar min ke. Allah ja da ranki farin cikina.* *MANZON ALLAH (SAW)* *Yace Kada kayi sallah a makabarta Kada ku zauna akan kabari* ************ Tana shiga dakinta! Ta shige bandaki tayo alwala. Kayan jikin ta ta cire ta saka kayan bacci. Sky blue din riga da wando ne, wanda suke hade da hular su. Kan gadonta, ta haye tana me yin Bismillah. Wayarta ta sa hannu ta zaro daga karkashi filon ta. Kunna ta tayi, Ido ta zaro, tare da daura hannun ta akan bakin ta, missed call din shi ta gani guda biyar. Murmushi tayi tana girgiza kanta. Tana kokarin kira sai ga kiran sa nan ya shigo. Murmushi tayi, ta dauka. Shiru sukayi ba wanda yace kala. Sun dauki wajen minti goma a haka, Sai numfashin su dake tashi kawai. Ido ta lumshe, Tana me tunanin kyakyawar fuskar sa. "Baby nah!" Yayi maganar da wata irin murya. Dan numfashin ta dake tashi ji yake kamar a jikin sa dumin sa ke sauka. Kiran sunan ta da yayi shi ya dawo da ita daga duniyar tunanin da ta lula. "Na'am!" Ta amsa da wata murya me rikita me sauraron ta. "Baby na ina kika shiga, duk na rikice. Gashi number su Mami na kira duk sunki shiga." Numfashi ta sauke, "Ayyah Yayana Dan Allah kayi hakuri, ina wajen Dady nah ne." Ajiyar zuciya ya sauke, "Dady ya dawo kenan." Itama ajiyar zuciyar ta sauke, tare da yin murmushi. "Eh!" "Ki gaishe shi." Ido ta lumshe, "Zai ji." Murya ya kara yin kasa da ita, "Baby na son ki zai haukatar dani fa." Ido ta bude da sauri, tare da zaro su ta mike zaune. "Ya Salam Yayana tayaya?" Wata ajiyar zuciyar ya sauke dan duk lokacin da *Asma'u* na magana tana kashe masa jiki ne. " *Husnah* son ki yayi mun kamu sosai. Baki ji yadda naji dana kira bakya nan ba. wallahi *Husnah* nasan bazan taba daina son ki ba." Murmushi tayi, tare da sauke ajiyar zuciya. "Shine kuma zai haukatar da kai." Tayi maganar cikin shagwaba. "Baki ji yadda naji a time din bane." Kai ta girgiza tana murmushi. "To am sorry Yayana Banyi dan na bata maka ba." "Kar ki damu nasan da haka. Nasan yanzu kuma ana gun Dady mantawa nayi na neme ki." Murmushi tayi. Ta lumshe idon ta, dan yana da saurin fahimta da bawa mutum uzuri. "Nagode da fahimta ta da kayi." "Nagode da son da kike min." Sukayi murmushi a tare. "To Baby kije kiyi alwala kiyi addua ki kwanta." "Toh!" ta fada tana tashi daga zaune da take. A speaker ta saka wayar ta wuce ban daki. Sai da tayi, addu'ar shiga sannan ta shiga. Alwalar tayi, sannan ta dawo Dakin. "Nayi Yayana." "To maza yi Addu'a naji muryar ki." "Toh!" Tace, ta bude tafukan hannayen ta ta fara karantowa. Falaki da Nas da Kul huwallahu Ahad Kafa uku uku sannan ta tofa a hannun ta ta shafe jikin ta dashi. Sai ta karanto Ayatul Kursiyu, sannan ta daura da amana Rasuli, *Bismika rabi wa da'atu. Janni wa bika arufa'uhu fa ina amusakutu nafsi daru jamha wa ina aru salutaha fa hufazuha bima tahufazu bihi ibadakal salihina* *Allahumma fina axabaka yauma tabu'asu ibadaka ×3* *Bismikallahumma Amutu wa ahaya.* *Subhanallah ×33* *walhamdililah ×33* *wallahu akbar ×34* *Allahuma Fadiri samaqati qal'ard raba kulli sha'in wa malikatu. Ashadu al la'illa anta a'uzu bika min sharri nafsi wa min sharri shaidanu wa shirukihi. Wa an aftalihu ala nafsi au adillahu illa muslim* "Shafe jikin ki ki kwanta da dama." Yin yadda ya umarce ta yayi sannan ya karanto mata shima. "Rufe idon ki." Rufewa tayi, "to kiyi bacci me dadi tare dani." Murmushi tayi tana gyara kwanciyar ta. Kissoshi ya dinga karanto mata. Tin tana ji har bacci ya dauke ta. Sai da ya tabbatar tayi bacci sannan ya kashe wayar sa. Alwala yayi yai addu'a ya kwanta da tunanin Babyn sa a ransa. Karfe sha daya Mami ta leko dakin nata, bacci ta same ta tana yi. A gefen ta ta zauna, kanta take shafawa ta zuba mata ido. Ido ta lumshe sannan ta bude. Addu'a ta kara tofa mata ta ja mata bargo ta fita tare da rufe mata kofa. Karfe biyar da kwata, ta mike, ban daki ta shiga tayo alwala. Tana fitowa, taji karar wayar ta. Murmushi tayi da taga me kiran nata. "Asssalamu Alaikum!" "Wa'alaikum salam My Ra'isul khalbi." "Kin tashi kenan." "Eh na tashi." "Masha Allah kije kiyi ibada kiyi mana addu'a." "Insha Allah!" Kan sallaya ta zauna sallah tayi raka'a biyu sannan ta dauko alkur'ani. A dai dai lokacin Mami ta shigo dakin nata. Akan sallaya ta ganta tana rairo karatun al kur'ani. Ganin tana karatun yasa ta juya ta fita. Jin za'a fara kiran sa yasa ta mike tayi raka'atanil fijir. Tana idar wa ta mike tayo sallah. Ta jima tana addu'ar sannan tajawo kur'anin ta ta cigaba da karanta wa. Sai da takai izifi biyu sannan ta mike ta dauko littafin makarantar boko tayi bitar karatun ta. Tana son karatun bayan magariba dana asuba dan in ta karanta ji take, kamar an bude kan ta an zuba mata dan sauki da yadda take fahimtar sa. Sai shida da rabi ta sauka kasa. Ko ina tsab sai tashin kamshi yake yi. Murmushi tayi, Mamin ta akwai tsafta da son kamshi. Kitchen ta shiga, Mami ta gani tana gyara nama. Murmushi tayi, ta karasa. Durkusawa tayi sannan tace, "Mami ina kwana?." Juyowa Mami tayi, ta kalle ta tare da yin fara'a "Kin tashi lafiya?" "Lafiya lou." "Kawo na taya ki." "A'ah jeki wajen Jamila, ki amso dankalin dana bata ta feraye." "Toh" ta amsa, Fita tayi wajen masu aikin gidan ta karbo ta dawo. kara wanke shi tayi sannan ta soya shi sama sama. Ta tsame shi ta kada kwai ta zuba kayan hadi ta dinga dibar soyayen dankalin tana zubawa cikin kwan tana soyawa. Tana gamawa ta hadawa Dadyn ta kunun gyada da yaji madara yai fari tas da shi. Tana gamawa ta gyare kitchen din sannan ta wuce sama. Dakin ta kara gyara wa ta saka room freshner da turare da dadi sanyin AC dakin nata. Kayyan jikin ta ta cire, ta shige ban daki danyin wanka. Sai da ta fara wanke bandakin ta sannan shima ta bade shin da kamshi. Sannan tayo wankan. Tana fitowa ta tsane jikin ta, mai ta shafa, sannan ta hade jikin ta da kamshi. Body spary ta dauko na Alharaman da na man sa ta shafe jikin ta dasu. Hoda kawai ta shafa sai kwalli da ta saka ya kara fito mata da manyan idanun ta. Sai man lebe da ta saka shima, ya amshi leben ta. shirya wa tayi, cikin wata, bakar doguwar riga da akai mata ado da ruwan hoda. Ruwan hodar mayafi da takalmi ta dauko, sai bakar jakar ta. Dakin Dady tayi, "Dady ina kwana," Ta fada tana karasawa wajen sa. "Lafiya lou *Husnah tah* " Tea da yake hadawa ta karba ta karasa hada masa. Fulas ta bude ta zuba masa soyayen dankalin da tayi sai, farfesun duk ta hada masa. Dankali ta dauka guda daya taci. "Dady na tafi." "Ina zaki?" "Makaranta." "Kin karya ne?" "In naje naci a makaranta." Fuska ya bata. Dawo wa tayi, "Menene Dady?" "Zauna kici kinji ko?" "Toh," Ta fada tana daukar kofi zata hada tea. "Karbi wannan." Murmushi tayi, "A'ah! Dady gashi ma zan hada." "Toh!" Tana gama hadawa ta saka hannu suna karyawa. Kadan taci ta zare hannun ta. "Dady na koshi." "Haba *Husnah* wai meyasa bakya son cin abinci ne." Murmushi tayi "Dady duk abincin da naci." "Kina cin abinci kinji yar gidan Dady." "Insha Allah Dady nah." Mami ce ta fito daga daki. "Iyye wai meyasa kike son kina deben ladan nawa, kici nawa kije kici naki." Murmushi *Asma'u* tayi, "Mami duk abinda nayi na bar miki ladan." "Toh kinji dai." Dady ya fada. "Naji amman tana bari na ina yin aikina." "Da kika samu me son yin aikin ma." "Rabu da ita dai Dady, haka take cewa in nayi aure bata san ya zatayi ba duk ta sangar ce fa." " 'Ka niyar ki. Yaushe na ke fadan haka." "Haba Mami kin manta ne." "Ina ji dai!" Ta fita. Tana dariya, "Dady bari naje kar na makara." "To *Husnah* a dawo lafiya." "Allah yasa," "Karbi wannan." Juyowa tayi, "Dady ka barshi da kudi a hannuna." "Haba *Husnah* ki karba, kika san wanda zai nemi taimakon ki kuma kika san abinda zai taso miki na kudi." "Toh Dady nagode Allah kara budi ya jikan mahaifa." "Ameen! Ameen! *Husnah* " "Na tafi Dady nah." "Allah kiyaye hanya. Ayi karatu da kyau." "Insha Allah." Dakin ta ta wuce, ta dauki jakar ta. ta dauki waya tayi. ta dauki hoton kanta. Dakin yayan ta, ta wuce. Yana kwance akan gado ya rufa da bargo. Murmushi tayi ta karasa kan gadon nasa. Yaye masa rufar tayi, "Yaya nah!" Ta kwala masa kira a kunnen sa. A gigice ya mike. Kallon ta ya tsaya yi. Baya taja. Tana murmushi. "Ina kwana Yayana." Hararar ta yayi, "Allah *Husnah* ki shiga hankalin ki, ina bacci kizo ki tashe ni." "Yi hakuri Yayanah, makaranta fa zan tafi shiysa naxo na gaishe ka." "Wai ke tin yaushe na fada miki bana son kina tadani ina bacci." Wayar tace tayi kara, tana dubawa taga Zainab ce. Murmushi tayi ta dauka. "Besty ya aka yine." "Kin tsaya tsokanar taki ko? Bayan kinsa Yau Sir Sabir ne damu kuma kinsan baya bari a shiga in an makara, ki kalli agogo karfe tara saura minti goma fa." Ido ta zaro, "Wayyo Sis gani nan." Ta fice a dakin da sauri. Mami taje taiwa sallama sannan ta dawo dakin Ya Buhari. "Ya please! Kazo ka kaini wallahi Baba baya sauri." "Naki." "Dan Allah!" Ta fara masa magiya. Har da su zubewa a kasa. "Tashi muje." yai gaba tabi shi a baya. *pls don't forget to vote* Tnc *INDABAWA* [1/18, 13:55] Maryam S Indabawa🥰: *ASMA'U HUSNAH* BY *MARYAM S INDABAWA* *MANS* 🌐HAJOW📝🌐 👩‍👧‍👧👩‍👧‍👧👩‍👧‍👧 HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS✍🏾✍🏾✍🏾 *11-15* DEDICATED TO MY WHOLE NUMBER *MOMMY* ALLAH YA FARANTA MIKI YA KARA MIKI LAFIYA DA NISAN KWANA YASA KI GAMA LAFIYA. ALLAH JIKAN IYAYEN KI *AMEEN* *Manzon Allah (SAW) Yace, "Indan dayan ku zai ci abinci. Yaci da dama. Idan dayan ku zai sha ruwa yasha da daman sa."* *Wallahi a littafin nan nasha fama dan na rubutashi tsab duk ya goge. Sai da na kara wani abun duk ba kamar wancan ba. Sai dai nayi kokari ganin na tuno amman wani dole na manta shi.* Ina gaishe ki Anty Rash da fatan alheri. Allah ubangiji ya dafa miki Ameen. Amman muna jiran cigaban *Yafi dare dugu* a taimaka mana* Dole na yabe ki AMRAH A MASHI PrincessAmrah. Gaskiya littafin nan Amrah nake so yayi kina kokari Allah ubangiji ya dafa Allah yasa a gama lafiya *Ameen.* Suna shiga mota, Aka kira ta. Dagawa tayi, da fara'a akan fuskar ta. "Assalamu Alaikum!" Ta fada dauke da murmushi. "Wa'alaikum salam!" Aka amsa mata daga can bangaren "Ina kwana Yaya nah!" "Lafiya lou. Kin fita dai ko." "Gani a hanya." ta amsa masa"Ina hoto nah?" y a tambaya. "Bari na turo maka. Ina nawa?" Ta fada tana lumshe ido. "Naki yana can yana jiran ki." ya bata amsa. "Masha Allah ganawa nan zuwa." Ta kashe wayar. whatsapp ta hau tayi masa sending pics din da ta dauka. Nasa ta fara budewa, kallon wayar ta zubawa idanu. Wani hoto ne ya bayyana, akan wayar ta. Wani hadaden Balarabe ya bayyana, yana sanye cikin bakar suit, idon sa sanye da farin gilashi. "Masha Allah! Yayanah kayi kyau." Ta tura masa. Amsa ya turo mata. "Tabarakallah! Allah nagode maka da ka bani wannan kyakyawar yarinyar Allah ka mallaka min ita." "Ameen Ya Allah Yaya na. Ka fita ne." "Gani a hanya." "To kaje ka duba mutane sai anjima." Ta fada. "Toh ki kular min da kanki kar ki bari kowa ya kalli fuskar ki." "Hmm ka kular min da kanka nima." Ta sauka a online. Titi ta kalla. "Haba Yaya." "Mene?" Ya tambaya yana kallon ta. Fuska ta dan bata ta ce, "Baka sauri fa." Murmushi yayi ya ce, "Karbi tukun." "A'ah yi hakuri. Amman dan Allah ka dada sauri kaga har tara tayi." ta fada tana marairaice masa fuska. Sauri ya dada sukayi gaba, yana direta ta bude kofar da sauri. "Nagode Yayana ka bada sako ga Besty nah." Ta fada tana murmushi Hararar ta yayi. "Ban da wayar ta ne ko baki." "Allah sarki Yayanah ji zanyi ko da gyaran da zan maka ne dan nasan na fika iya love." ta fada tana kanne masa ido daya. Kokarin bude kofa yake ya fito. "Yi hakuri!" Ta fada tana yin gaba da sauri. Kofar ajin ta karasa. Wani kyakyawan saurayi ne a ciki baki ne amman yana da kyau ba kadan ba. Sai kayi tsamanin irin black american nan ne. Sanye yake da farar shadda kansa ba kula sai gashi da ya kwanta luf luf akan sa. Lekawa take yi jifa jifa. Ganin sun hada ido yasa tai saurin dauke kan ta. Fita yayi ya zuba mata ido. Kai ta dukar kasa. Kallon ta ya cigaba dayi. "Wa kike nema." Ya tambaye ta da turanci. "Uhmm daman yanzu nazo ne." ta bashi amsa tana in ina. "Shine kuma me?" Ya tambaye ya. "Ba komai." Ta fada jiki a sanyaye "Karfe nawa kuke da lecture?" Magana yake cikin turancin da ya kware a bakin sa. "Sir karfe tara." ta fada masa kan ta a kasa. "What say's d time now (Karfe nawa yanzun)." "Ban sani ba." Kallon ta ya tsaya yi. Sannan ya duba agogon hannun sa. Karfe tara da rabi. "9:30am yanzu ne lokacin zuwan ki." "I am sorry Sir." "Naji daga yau kika makara kar ki kara dosan kofar ajina kinji ko?" Kai ta gyada masa. Kanta a kasa taki yadda su hada ido dan wani kwarjini yayi mata. "Shigo ciki." Ya fada yana yin gaba A gaban allo ya tsaya tayi hanya zata shige ciki. "Come here (zo nan)," Ya fada yana nuna mata wajen da zata zauna. A gaban sa. Komawa tayi ta zauna, duk dagowar da zatayi idon sa na kanta. Kuma duk tambayar da zaiyi ita yake jefawa. Sosai take bashi amsa dan *Asma'u* akwai kokari. Sai karfe sha daya yabar ajin nasu. Tana zaune a inda take zaune sai ga Zainab ta karaso wajen ta. " *Asma'u* amman fa kinyi sa'a har malamin nan ya bar ki kika shigo." "Nima nayi mamaki dan kinsan haka yan wacan shekara suka sha fama dashi." "Dan Allah kina dai kula." zainab ta fada cikin damuwa dan bata son kawar tata ta rasa aji. "Kar ki damu yau ma akasi aka samu ne." Wani malamin ne ya shigo musu, yai musu lectures dan sai karfe daya ya fita. Yana fita suka shige, masallaci. Sai karfe daya sukai sallah sannan sukayo cafeteria. Lemo kawai ta karba, sannan ta tambayi Zainab me take so. Ta siya mata. Suka samu wajen zama. "Sis wannan gayen fa ya dame ni da maganar ki." Murmushi *Asma'u* tayi, "Wane gaye fa." Hararar ta Zee tayi, "Wai har kin manta." Asma'u ta ce, "Wallahi na manta." Zee ta ce, "Wannan Nasir din dan unguwar mu." Murmuahi Asma'u tayi ta ce, "Oh na tina. Ya akayi." Dan hararar ta zee tayi ta ce, "Wallahi ya dame ni ne." Kallon Zainab Asma'u tayi ta dan saki murmushi ta ce, "Ki bashi hakuri kinsan dai irin karatun da muke ciki ko?" Zainab ta ce, "Haka ne, amman ai karatu mun gama tinda asibiti zamu tafi, ya kamata ki maka ma miji da mun kammala sai mu shige gidan mu ko." "Haka ne Zee amman nifa nayi karama da yawa!" Hararar ta Zee tayi. "Shekara sha tara din shine kike karama. Da da akewa yan shekara goma aure fa suce me." "Haka ne, Sis ina tsoron aure ne, kuma dai bari kinji na fada miki. Nayiwa kai na miji kuma nasan shi zai fahimce ni ya kuma gatan tani." Murmushi Zee tayi, "Masha Allah wane wannan." "Ya Aslam mana." Asma'u ta bata amsa tana lumshe ido. Dariya Zainab ttayi ta ce, "Wane ma Ya Aslam." "Ke Zee har kin manta shi. Dan gidan Yayar Mami nah fa. Ta Abujar nan." "Oh nagane shi. Abinda har gida sun zo tare da Love dina." Murmushi *Asma'u* tayi. "Dan haka ki bashi hakuri. Nasan Nasir nada hankali da ilimi komai dai ya hada. Amman ki bashi hakuri." "Ba komai zan san yadda zan sanar masa insha Allahu." "Nagode." "kar ki damu." Wayar tace tayi kara, Tana dubawa ta saki murmushi ta dauka. "Assalamu Alaikum Baby " aka dada daga can bangaren "Wa'alaikum Salam." Ta amsa masa murmushi dauke a fuskar ta. "Kina lafiya dai ko?" Ya tambaya. "Lafiya kai fa?" "Lafiya Alhamdulilah da fatan kinyi sallah kinci abinci." "Yaya duk nayi biyu nake jira tayi mu shiga aji." "Masha Allah abinda na kira naji kenan." "Nagode da kulawar ka." "Ba komai." "To kai kaci abincin da sallah " Na dai yi Sallah abinci kuma sai na gama aiki zan ci." "Kai Yaya!" ta fada a shagwabe "Yi hakuri befi mutum uku ba kinji " "Da gaske." "Eh!" "To dan Allah kana gamawa kaci." "Insha Allahu!" "Yauwah nagode." "To sai ajima ko." "Aha bye." Ta katse wayar. Zainab ce ta kalleta. "Kece kuwa *Asma'u* " "Me nayi?" "Soyayya " "Haba Aunty Zee ina wata soyayya anan. In ma soyayya ce ke kika koya min ai." "Ni kuma?" "Eh man yadda ko da yaushe kike yi a gabana." Dariya tayi, "Tashi mu tafi." "Toh!" Suka tafi hall din da zasuyi lectures. Tinda suka shiga sai bayan hudu suka fito. Suna fitowa sallah sukayi su. Lokacin har anzo daukar Zainab dan haka ta tafi ta bar *Asma'u* tana jiran azo daukar ta. Ba tayi minti biyar da zama ba, aka zo daukar ta. Tana mota Ya Aslam ya kira ta. "Baby nah ya makaranta." "Gani a hanyar komawa gida." "Sannu kin gaji ko?" "Wallahi, na gaji jikina sai ciwo yake min" "Sannu kinji ai da ina kusa da nayi miki tausa ko." Murmushi kawai tayi. "Yaya nah kai fa ka tashi." "Ina fa, aiki ma zan fita yanxu." "To Allah bada nasara." "Ameen! Sai anjima." Ta kashe wayar. Idon ta ta lumshe, gaskiya tayi sa'a samun Yayan ta a matsayin me sonta, wanda tasan tin kafin ya fara son ta yake kula da ita da riritata bare yanzu kuma. A rana sayi waya sau nawa banda text din safe na rana da na dare. Yayanta na son ta sosai da duk tafiyar da zaiyi tsarabar ta daban ce. Haka nan Ga soyayyar Dadyn ta da itama take kara sa mata nutsuwa. Tana shiga gida ta tadda Mami a kitchen dan haka kitchen ta shige ta fara taya ta aiki. Sai gab da magariba suka gama sannan ta mike ta hau sama. Wanka tayi ta saka kaya mara sa nauyi. Turare ta feshe jikin ta sanna ta hau kan sallaya tayi sallah. Tana idar wa ta dauko kur'ani ta fara bita sai da ta kai ixifi daya sanna taji kiran sallah isha'i mikewa tayi, tayi sannan ta fita zuwa falo. pls don't forget to follow and vote @ msindabawa Nagaishe ki ummu Ayda Allah bar mu tare Ameen *INDABAWA* [1/18, 13:56] Maryam S Indabawa🥰: *ASMA'U HUSNAH* BY *MARYAM S INDABAWA* *MANS* Facebook @Indabawa novel Wattpad @Msindabawa Insta @Maryam S Indabawa *HAJOW* � *HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS* � *16-20* DEDICATED TO U *MOMMY NAH* NO ONE LIKE U IN MY LIFE REALLY LOVES YOU *MY HAPPINESS* *Manzon Allah (SAW) ya ce, "Kada dayan ku yayi tafiya da takalmi guda daya. Ko ya saka duka. ko yacire baki daya" Kamar kullum sai bayan isha'i na sauka. Da fara'a ta na karasa wajen Dady na. 'Barka da dawowa Dady ya aikin?" Murmushi yake ta zubawa. "Yauwah *Husnah tah* aiki lafiya Alhamdulillah! Ya makarantar." "Makaranta lafiya Dady." "Masha Allah!" "Dady tashi muje kaci abinci kaxo ka huta." "Toh yar gidan Dady." Suka mike. Wajen Mami ta karasa, "Mami taso." Itama mikewa tayi, sai tayi wajen Ya Buhari, "Babban yaya taso" Baki ya tabe ya mike. Gefen Dady ta koma ta kamo hannun sa ta hade dana Momy, suka nufi gun cin abinci. Sai da ta zubawa kowa sannan ta koma gefen Dady, "Yau tare zamu ci." Suka fara cin abincin su. Suna gamawa tayi kitchen dasu ta wanke sannan ta dawo falon. Tausa takewa Dady a kafafun sa, yana tambayar ta harkar makaranta. Karfe tara tayi dakin ta bayan ta gama tsokanar yayan ta tayiwa Dady da Mami sai da safe. Tana shiga wanka tayi tayo alwala sannan ta murje jikin ta da mai, me kamshi tasaka kayan bacci a jikin ta. Gado ta hau tana me janyo wayarta da ta ajiye. Ido ta lumshe lokacin da tayi tozali da hoton Ya Aslam akan wayar ta. Fita tayi daga galleryn ta duba screem din wayar sakon sa ne akai. Dubawa tayi. "Love na dawo gida amman tunanin ki kawai nake. Ji nake dama anyi auren nan muna tare da na shigo nayi tozali dake." Murmushi tayi, "Yaya nah ina sonka." Ta fada tana mai kiran number tasa. Bugu daya ya dauka. "Hello Habibaty." "Uhmm Honey, ya gajiyar aiki." "Ruwan zafi ya tafiyar da ita. Kinga da munyi aure ke zaki gusar min da ita." "Rai dai wani lokacin ni zan gusar da ita." "Wayyo Allah! Da kuwa naji dadi. Allah nuna min wannan lokacin." "Ameen!" "Fadan me dame zakina min in munyi aure." Ido ta rufe da hannayen ta, dan sai taji kunya. "Yaya nah sai anyi aure ka gani." " *Husnah* kenan baki san yadda nake son ki ba. Na miki alkawarin bazan taba rabuwa dake ba." "Nima na maka alkawarin baxan taba juya maka baya ba duk abinda zakayi min." " *Husnah* zan gatataki na nuna miki tsantsar soyayyar da nake miki. Baxan taba barin ki kiyi kuka ba." "Nima insha Allahu zaka same ni mai kula dakai da kuma faran ta maka." "In kuwa har hakan ta kasance nasan zaman mu zai yi dadi." "Allah tabbatar mana da alheri." "Ameen Baby nah. A tashi aje ayi alwala azo ayi addu'a ki kwanta." A speaker ta mai da wayar, taje tayo alwala ta dawo tayi addu'a duk yana jin ta, ta gama Ta shafe jikin ta. Kissar Annabi Musa ya ke bata, tin tana ji har bacci ya duke ta. Sai da ya tabbatar tayi bacci sannan ya kara karanto mata addu'a, sannan ya mike yayo alwala yai sallah ya kwanta yana me karanto addu'ar ya tofe jikin sa da ita. Kamar yadda ta saba karfe biyar da biyar da kwata ta tashi alwala tayo tazo tayi raka'atanil firji. A lokacin Ya Aslam ya kirata. "Baby nah kin tashi dai ko." "Eh na tashi." "Kinyi sallah ko." "Nayi ai tinda ka kara fadan darajar ta ban kara fashin yin ta ba." "Masha Allah. Sai anjima." Ya kashe wayar Sannan ta mike lokacin da ana kiran sallah tayi sallah. Karatun al kur'ani sannan ta dauko littafin makaranta tana dubawa. Mami ce ta leko ta ganta ta dukufa akan littafin ta, Murmushi tayi ta juya. Tana son *Asma'u* yarinyar akwai shiga rai da neman ilimi tare da ladabi da biyayya. Sai karfe shida sannan ta fita. Falon su a gyare sai kamshi yake da ke Mami da ta tashi take gyara wa. Dan bata yadda da masu aiki suna gyara mata cikin gida ba. Kitchen ta nufa. Mami ta tadda har kasa ta durkusa ta gaida ta. Doya taga ta sauke, karba tayi ta fara soyawa sannan tabar kadan tayiwa Dady yamball da ita. Sai kunun gyada da ta dama masa. Ta kai komai sama. Sannan ta dawo ta taya Mami gyara kitchen din. Sannan tayi sama. Dakin ta, ta gyara ta share sanna ta wanke bandakin ta feshe shi da turare ko ina. Wanka ta shiga tayi ta fito ta shafe jikin ta da mai sannan ta murje jikin ta da humra. Katuwar doruwar ta. ta bude, Kasa ta duka ta dauko kayan cikin ta. Sanna ta mike ta dauko wata bakar riga me adon ja. Sai jan mayafi da ta dauko. Babba dashi. Shiryawa tayi bayan ta saka kayan ta kama gashin ta tayi parking nasa. Jar hula ta saka sannan ta dauko mayafin tayi rolling nashin. Ta dauko turaren ta, ta fesa. Jakar ta ta dauko ta zuba duk abinda take bukata. Sannan ta dauko wani cover shoe takalmin ta ja tasaka. Fita tayi ta nufi dakin Dady, yana hango ta ya saki fara'a. "Dady ina kwana?" "Lafiya lou *Husnah* kin tashi lafiya?" "lafiya lou." "Har kin shirya kenan." "Eh Dady." Mami ce ta fito daga dakin Dadyn ita ma taci adon ta tayi kyau. "Matsa na hada masa abinci." "Mami bari na hada masa." Kunun da ta dama ta dauko masa ta zuba sannan ta juye masa madarar ruwa, ta mika masa. Sai doyar da yam ball da ta zuba masa. Tea ta hada ta fara sha. Ta dan tsakuri doyar taci. "Wai *Husnah* baza kina cin abinci ba ko?" "A'ah Dady wallahi dana fara cin nake jin ciki na ya cika." "Kina son na fara miki dura ko." "Ah yoh *Dadyn Asma'u* ai kaima gara ka gane bata son cin abinci." "Kai Mami." "Karya zan miki." "A'ah!" "Toh ya isa, ke *Husnah* kina cin abinci kinji ko." "Naji Dady." "Allah miki Albarka." "Ameen!" Hira suka dan taba sannan ta masa sallama ta mike. Kudi ya kara bata kamar kullun sai taki amsa haka kuma dole zai sa ta amsa dan ko wani zai nemi taimako a gun ta. Jakar ta, ta dauko, ta shige dakin Yayan ta. Baccin sa yake hankali kwance. Bude shi tayi ta dinga daukar sa hoto. Sai da ta gama sannan ta tashe shi. "Ooo *Asma'u* Allah kada ki bari na tashi." "Haba Yaya ai kai ma kasan bazan iya tafiya ban gaida ka ba." "Naji nagode dan Allah jeki." "Please ka tashi kaga princess din taka mana." " *Asma'u* " ya kira ta da babbar murya. "Na'am!" "Tafi nagode!" Bargon da ya rufa dashi ta yaye sannan ta fita a guje. Bayan ta yabi da gudu shima. Dakin Mami ta fada tana. "Mami kingan shiko." Tayi bayan ta. "A'ah fah *Asma'u* kin cika tsokana kin qi dai ki girma ko." "Mami shikenan bazan je na gaida Yayana ba. Bayan tin muna yara ake cewa muna gaida na gaba damu." "Oh sai akace in yana bacci ma a tashe shi a gaisar." "To Mami dan me bazai tashi ya wuce aiki ba ko dan yasan a karkashin Dady yake aiki." Dai dai lokacin da ya shigo dakin. Kara kamkame Mami tayi tana ihun ta taimake ta "A'ah a'ah Buhari rabu da ita kayi hakuri kaji." "Haba Mami kullum sai ta tada ni ina bacci." "Yi hakuri kaji baza ta sake ba." Lokacin wayar ta ta fara qugi. Da sauri ta dauka. "Baby kindai fita ko!" ya tambaya daga can site din. "Yanzu zan fita." Ta fada tana kallon Mami. "8:30 fa kina kuma da lecture 9 me kika tsaya yi." ya tambaya. "Yi hakuri na tafi." Ta fada tana diba a guje, tana cewa "Mami na tafi. Yaya kayi hakuri sai na dawo." "Tafi dai a hankali. Kar ki fadi." Mami ta fada. "Allah ya kara kullun sai ta tsaya tsokana taje ta makara." Yayan ta Buhari ya fada. "Ya Aslam na fito." Asma'u ta fada bayan ta fita compound din gidan. "To daina gudun kada ki fadi." Ya fada cikin tausasa murya. "Toh!" to ta amsa. "Tsokanar kika tsaya ko?" ya tambaya dan yasan hali. "Yaya kaima tsokanar zaka ce ina yi zuwa nayi fa mu gaisa." Tai maganar cikin shagwaba wacce ta riga ta zame mata jiki kasancewar ta Autah. "Kuma yana bacci kika tashe shi ko?" Ya fada daga can barin. "A'ah fa." Ta fada masa tana karasawa wajeen motar gidan su, "Ki daina dai." "Toh!" ta amsa. "Bari mayi magana anjima." "To a dawo lafiya." Ya ce, "Ni tin dazu ina office. Ke zan cewa a dawo lafiya ayi karatu." "Insha Allah!" "Bye!" Tana karasawa Baba driver ya tashi ya bude mata. "Baba nagode." Ya shiga gidan gaba yaja suka tafi. Sai daga baya ta samu ta gaida shi. cikin sa'a tara saura minti biyar ta shiga makaranta. Da sauri ta karasa hall din da suke daukar darasi. Tana shiga har Zainab ta sama mata wajen zama.. Don't forget to vote @MSIndabawa *Indabawa* [1/18, 14:05] Maryam S Indabawa🥰: *ASMA'U HUSNAH* BY *MARYAM S INDABAWA* *MANS* 🌐HAJOW📝🌐 👩‍👧‍👧👩‍👧‍👧👩‍👧‍👧 HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS✍🏾✍🏾✍🏾 *21-25* DEDICATE TO *MY LOVELLY MOMMY* UR LOVE IS SPECIAL. MAY ALLAH BLESS YOU *AMEEN* *Manzon Allah (SAW) Yace "Zagin musulmi fasikanci ne. Yakar musulmi kafirci ne"* Sai bayan sun fito Zainab ta samu damar yi mata korafi. "Wallahi ke dai kin baci yanzu." "Da me?" "Makara mana. Gobe dai Sir Sabir ne." Murmushi tayi! "Ki kwantar da hankalin ki da wuri zan fito." "Allah yasa." "Ameen!" *-*-*-*-*-*-*-*-*-*-* Zaune yake cikin office din shi ba abinda yake sai tunanin ta duk inda ya juya hoton fuskarta kawai yake gani. "Ya Salam! Allah ka dauran abinda zanyi dashi." Ya fada yana jinginar da kan sa a jikin kujerar da yake zaune. Yarinyar tayi min, irin ta nake son aura. Gaba daya ta gama tafiya dani. Ido ya lumshe yana tuna maganar Mamahn sa. "Sabir kana girma amman har yanzu kaki ka kawon matar aure ko, ga yan mata nan a family amman duk kaki ka kula su ko." "Mamah ki kara min affuwa na kusa kawo matar da zan aura." "Allah nuna min." "Ameen!" Ajiyar zuciya yaja. "Insha Allahu na samu mata." Ya fada yana bude firij din gefen sa ya dauko lemo. Haka ya koma gida sukuku dashi duk ba wani karfi a tattarre dashi. Yana shiga Mamahn sa tasan da abinda ke damun sa. "Sabir lafiya dai ko?" Murmushi ya kakalo. "Lafiya lou Mamah." "Ka tabbata." "Eh!" Ya fada yana daga mata kai. "Taso kaci baccin ka kaji." "Mamah sai anjima." "Sai anjima" ta tambaya dan tabbatar wa "Eh!" Ya amsa mata. "Allah ya kyauta." ta fada. Tana kallon sa. "Abbu ya dawo ne?" Ya tambaya. Mamah ta ce, "Yana dakin sa." Sabir ya ce, "Ohk bari naje na dan huta in na fito ma hadu." Kallon sa ta tsaya yi, saboda tasan indai Abbu na nan ba abinda ke rabasu da gudu zaiyi wajen sa. Kai ta jinjina Tana me masa Addu'a a cikin zuciyar ta. Wata kyakyawar farar yarinya ce, doguwa ce, siririya amman sam bata da shape. Zaune take a katon falon ta kayan marmari ne a cike a zube sai wata kawar ta dake gefen ta. "Preety wai ya zancen Aslam kin shawo kansa dai ko." gyara zama wacce aka kira da Pretty tayi. Ta ce, "Ina fa, abi ya ci tura." "To yanzu mene abin yi." "Wajen Malamin nan nake son zuwa. Wallahi bazan iya rasa Aslam ba shi ya nacewa karamar yarinya kome tafini dashi oho. Amman wallahi sai na raba su." preety ta fada. kawar tata tace "Preety ina bayan ki. Amman ina zakije wajen malamin?" "Kinsan gobe zamu tafi Dubai ni da Moma. To da mun dawo zan shirya zuwa nijar." "Allah dawo daku lafiya." Kwance *Asma'u* take akan sofar dake dakin ta. Waya ce a kan cikin ta. Sanye take da dogon wando, sai riga purple wacce da kadan ta wuce gwiwar ta. An mata ado da stones sai kwalli suke yi. Kanta hula ce baka. Idon ta a lumshe sai kace me bacci. "Kina jina." Ya fada daga cikin wayar. Sai da ta sauke ajiyar zuciya sannan. Ta amsa masa da. "Eh! Ina jinka." Ya cigana da fadin. " *Husnah* wallahi kin sacen zuciya ta gaba daya. Ban da tunani da buri in ba na na mallake kiba." Shiru tayi, "Wallahi zan iya sadaukar da kome nawa dan samuwar farin cikin ki. Na miki alkawari ba abinda zai raba mu sai mutuwa." "Yayanah na yadda dankai kuma nasan kai me sona ne. Nima bazan taba barin ka ba ko juya maka baya ba." "Nagode *Husnah* Allah miki albarka. Allah mallakamin ke." "Ameen Ya Allah!' Aslam ya ce, "Toh yanzu me kike." Asma'u ta ce, "Ina kwance ne." Aslam ya ce, "To maza tashi kije kiyi alawala kinga magariba ta kusa kiyi ta lazumi." Asma'u tayi murmushi ta ce, "Toh Yayanah." Shima murmushi yayi ya amsa mata da "Aha Sai Anjima." Mikewa tayi ta shige bandakin ta tayo alwala. Akan sallaya ta zauna tana lazimi. Sai da taji kiran sallah sannan ta mike ta tada. Tana idarwa ta dauko alkur'ani ta fara karantawa. Sai da aka isha'i sannan ta mike tayi sallah. Ta jima tana addu'a sannan ta shafa ta mike ta fita falo. Tin daga bene ta fara cewa. "Dady nah Oyoyo!" "Oyoyo *Husnah* ta." Ta sauko ta karasa wajen sa. "Dady Ina yini?" "Lafiya!" "Dady ya aiki." "Lafiya Alhamdulilah! Ya makaranta." "Makaranta lafiya Dady!" "Masha Allah! Badai wata matsala ko." "Babu!" "To Allah yayi albarka." "Ameen!" Ta juya wajen Ya Buhari. "Ah Na Anty Zee barka da dawowa." Hararar ta yayi ya dauke kai. Dariya ta saki. "Dady kaga ina masa sannu da zuwa ya harare ni." Murmushi Dady yayi, ya ce, "Wai wace Zee din nan ne?" "Sis yi hakuri dan Allah!" Ya Buhari ya fada yana marairace mata. Asma'u ta kanne ido daya tace, "Yo Dady ai ka gane kawai." kai Dady ya dan daga ya ce, "Oh nagane yar gidan Dady." Suka yi dariya gaba dayan Dakin. "Ai ni gara ya kawon surikar wallahi." Mami ta fada tana kallon sa. Shi dai kasa yayi da kansa kawai. "Ai fah!" Dady ya fada yana kallon *Asma'u* Gira ta dage masa. Suka saki murmushi tare. "Uhmm Abban nah tashi muje kaci abinci." Ta kama hannun sa. "Mami ku taso muci abinci." "To!" Kamar kullum bayan tagama tsokanar Yayan ta ta haye sama. Tai wanka tayo alwala ta shirya cikin kayan baccin ta. Kwanciya tayi tana jiran kiran sa. Ai kam ko minti uku batayi ba sai ga kiran sa nan. Murmushi ta saki wanda ya kara fito mata da ainihin kyauwun ta. Muryar Aslam ce ta daki kunnen ta bayan ta kara wayar. ya ce, "Hello! Baby nah!' Gyara kwanciyya tayi ta ce "Na'am my Yaya." Murmushi yayi ya ce, "Ina matukar kaunar ki Habibaty." Asma'u ya ce, "Nima haka Yaya nah." Aslam ya ce, "Kinsan me?" kai ta girgiza kamar yana ganin ta ta ce, "A'ah!' Aslam ya danyi jim sannan ya ce, "Wani abu na gama tunani." Da sauri ta ce, "Na mefa?" Aslam ya ce, "Hmm tunani nayi a duk cikin duniyar nan duk cikar ta sai Allah ya hada mu a soyayya bayan nasan kin fini komai da komai. Allah nagode maka." Ajiyar zuciya ta sauke ta ce, "Haba Yayana me nafika, kai ma kasan ka fini. ni zan yiwa Allah godiya da ya hada ni da miji kamar ka." Aslam ya ce, "Baby kin wuce duk inda nake tunani. Ke ta daban ce. Haka son ki ma na daban ne a cikin zuciya ta." Ta ce, "Yayanah nima haka kake a zuciya kana da matsayin da ba wanda yake dashi a guna. Kana da gurbi na daban a cikin zuciya ta." Murmushi yayi. ya ce, "Kisani dake kadai zan so na rayu kuma na mutu. Har abadan da ke nake son na kasance." Shiru tayi! Tana me sauraron sa tare da lumshe ido fuskar ta na fitar da wani murmushi na nishadi da farin ciki. Ya cigaba da magana, " *Husnah!* Zuciya ta da taki abokan juna ne da basa taba rabuwa ko agun bacci Ido biyu ko a cikin bacci na ke nake tunani haka ma a fili. Wallahi son ki ya zama jinin jikina rabani dashi tamkar raba ni da rayuwa ta" Ido ta bude ta ce, "Yayanah na yadda dakai haka duk abinda zaka fada suma na yadda dasu. Kar ka damu insha Allahu ni taka ce har abada." Aslam ya ce, "Nagode *Husnah* zan miki alkawarin bazan taba rabuwa dake ko juya miki baya ba." Asma'u tace, "Nima insha Allah bazan taba barin kaba sai dai in har ka ka bukaci hakan." "Shittt!" Ya fada da karfi. "Indai nine bazan taba bukatar hakan ba." "Allah ya sa." ta fada a sanyaye "Baki yadda ba." ya tambaye ta "Haba dai na yadda da Yayanah. Kai dai kawai kace Ameen." Ta fada duk yanayin ta a sauye. "Toh Ameen ya Rabbi." "Yauwah ko kai fa." Dariya ya saka. "Lalai Baby nah. Kin mai dani kamar Baby ko." Murmushi tayi ta ce "Oh to mene in na maida kai Baby nah!" Dariya yayi ya ce, "Ba komai nasan zan sha gata ne ma." Ta ce, "Ashe ka gane." "Eh! Amman fa kece Baby." "Wai nice Baby shekarata nawa." ta tambaya taba turo baki Murmushi yayi dan yasan *Husnah* da son girma ya ce, "Ni a wajena ina kallon ki kamar yar shekara biyar dai dai lokacin da yara suka fi shagwaba da rigima." Baki ta bude ta ce, "Lalalah! Ni din biyar fa kace." Dariya Aslam yayi ya ce, "Eh man." Asma'u ta ce, "Yaya ka manta shekara tane." ya ce, "Shine nace a wajena ai." Ta ce, "Oh! Saboda me to?" "Saboda Babies abin rarashi ne da tarairaya da shagwabawa. Wannan yasa nake kallon Baby nah ahaka saboda na mata duk abinda na lissafa." "Oh inkuwa haka ne. Na yadda ni Babyn kace." Dariya yayi ya ce, "Yauwah Baby nah." "Toh nima kai Baby nane. Tinda ina son ina maka abubuwan da ka fada." " *Husnah* kenan. Dare yayi aje ayi alwala azo ai addu'a" "Toh" Ta fada tana mikewa. *Morning My Yan uwa* Hhh wai da gaske Asma'u life na burge ku. To haka ake so mutum ya kasance kar ya dulmiya da duniyar nan sosai. A komai kana riko da alkur'ani kariya ne gare mu sosai. Muna godiya da Allah yayi mu a matsayin musulmai kuma yake bamu ikin karanta sakonnin sa. Wanda duk karantawa da zamuyi muna samun lada mai yakai wannan dadi. Kana karantawa kana jin dadi da annushuwa da nishadi. Sai alkur'ani. Alhamdulilah *Muje zuwa* *INDABAWA* *love u wujiga wujiga masoya na.* [1/18, 14:06] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *ASMA'U HUSNAH* BY. *MARYAM S INDABAWA* *MANS* *HAJOW* *HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS* ✍✍✍ *Da farko ina mai bada hakuri dan zan canja sunan littafin nan daga *Asma'u Husnah* zuwa *labarin rayuwar Asma'u Husnah* wanda dalilin haka yasamu ne na wata yar uwa marubuciyya da tayi littafi mai suna *Asma'ul Husnah* wanda ni na canjawa nawa suna yanzu. Ina fatan xaku cigaba da karanta *labarin Rayuwar Asma'u Husnah* Nagode *26-30* Dedicated *FIRST AND LAST LOVE. MY MOMMY* *Manzon Allah (SAW) Yace, "Idan watan ramadan yazo ana bude kofofin aljanna ana rufe kulle shaidanu" (mu yawaita abinda zai samu samun rabauta duniya da lahira)* Da wuri ta kamala abinda zasuyi ta shirya tayi wajen Dadyn ta. Tare sukai break, sannan ta tafi. Da wuri ta shige ajin su. Text din Ya Aslam ne ya shigo. "Morning Pretty nah. Ya kike tin dazu nake son kiran ki. Nasan kina aiki. in kingama ki turon hoton ki. Sannan naje Lagos ne Dady ya aike ni. Ina bukatar addu'ar ki." Murmushi tayi ta maida masa da sakon. "Na tashi lafiya Yaya nah. Kaima ina fatan kana lafiya. Ya hanya. Hotona yana can na tura maka yana jiran ka." Ta tura tana murmushi, Zee ce ta taba ta, "Sis Lafiya kike ta zuba murmushi haka." "Lafiya lou wallahi. Kin karaso kenan." "Eh!" Dai dai shigowar malamin su. Sai karfe sha biyu ya fita wani ya shigo yai musu awa daya sannan suka tafi sallah. Suna fito wa suka shiga cafeteria suka siyo lemo da snack, a nan kofar hall din su suka zo suka zauna. Karkashin wata bishiya. A jaka suka saka abincin su dan ba lokacin zasu ci ba, kawayen su ne suka karaso wajen su uku. "Ah *Asmy* da Xee." Su ka fada suna dariya. Murmushi sukai masu, "Ya kuke?" "Lafiya lou. Ya karatun." "Alhamdulilah." "Masha Allah!" Suka zauna suna dan taba hira. Sai karfe biyu suka koma aji dan daukar wani darasin. Karfe hudu sun gama kowa yayi gida. *WACECE ASMA'U HUSNAH* *Asma'u* 'ya ce ga Alhaji Suleiman. Alhaji suleiman dan kasuwa ne duk da yana da kwallin masters a hannun sa. Ya karanci fanin kasuwanci. amman yafi sha'awar kasuwan ci da aikin gwamnati. Sai daga baya ne ya nemi aiki sannan yake hada kasuwanci da aikin nasa. Alhaji Suleiman dan gidan Malam Haruna ne, Malam Haruna malami ne, kuma dan garin kano ne. Cikin garin Madobi. Yana da matar sa daya Aisha, Allah ya azurta su da Ya'ya uku maza sai autar su mace. Alhaji Suleiman shine babba da matar sa daya hajiya Amina. Ya'yan su biyu, Buhari da *Asma'u Husnah* Sai Abubakar me bi masa, yana aiki a banki matarsa daya masa'uda, da ya'yan sa biyar duk maza. Abubakar, Suleiman, Abdulhakim, sai yan biyu. Dukkan su sun girma kowa ya kama aiki. yana zaune anan katsina shima. Ilyasu shima matar sa daya soja ne. Yana da ya'ya uku duk maza suna zaune a kaduna. Muhammad, sai yan biyu shima. Shima dukkan su sun girma suna aiki. Sai kanwar su kuma autar su Mariya wacce take aure a kaduna itama mijin ta soja ne. Ya'yan ta uku duk maza. Umar, Usman, Aliyu. Amina Maman *Asma'u* ta kasance yar aminin Kakan *Asma'u* wato Baba Haruna. Amina su biyu Allah ya bawa mahaifin ta Malam Isah da matar sa Hafsat. Da yayan su Fatima da Amina. Yayar ta na auren minister of Agriculture wanda suke zaune a Abuja. Aslam shi kadai ne danta. Wanda shi kuma yayi karatu a Kasar waje fanin asibiti wato medicine kwararen likitane. Amina da Suleiman sunyi auren soyayya ne wamda har yanzu suke shan soyayyar su. Zuri'ar ta kasance ba mace a cikin ta illa *Asma'u Husnah* *Asma'u Husnah* ita kadai ce jika mace ga Haruna da Isah, wannan yasa dukkan family din suke son ta da kaunar ta. Bama Aslam da yake da son yara. Dan da aka haifi *Asma'u* sai da kyar ya bar gidan shima dan makaranta ne. Soyayyar ta dai da ita ya tashi. Sai kuma Allah yayi *Asma'u* irin yaran nan ne masu shiga rai. Dukkan yan uwan ta son ta suke. Yarinya ce wacce tin da aka haife ta take da kyan ta duk da baka ce amman bakin ta me kyau ne su ake kira da black beauty. Dan *Asma'u* komai Allah ya bata. Shekarar ta biyu aka sa ta a makaranta. Inda tana da shekara biyar tana nursery two. Allah ya bata kokari duk da karancin shekarun ta inda aka dinga mata jumping din classes. Shekarar ta takwas ta gama primary ta tafi secondary. Tana da shekara goma sha hudu tayi candy. A lokacin Ta fara girma dan ta fara kirgar dangi. Kyawun ta ya dada fitowa. Tana yin candy ta samu admission inda take karantar medicine yanzu haka Asibiti zasu tafi. Tin tana primary ta sauke alkur'ani inda yanzu haka tana da haddar sa akai. Kuma bata daina yi ba. tana kanyi dan duk juma'a take bawa Mamin ta haddar. Karatun ta baya hana ta haddar ta. Kamar yadda duk asabar da lahadi take zuwa isilamiyya da safe. *Asma'u* yarinya ce me fara'a da barkwanci da son jama'a. Koma abin hannun ta be rufe mata ido ba. Akwai tarbiyya dan duk yadda mutum ya girme ta zata bashi girman sa. Akwai ta da son zumunci. A duniya tana son Dadyn ta kamar yadda shima duk duniya bai da wacce yake so irin ta. Kullum bata da buri sai na ganinnta kyautata masa. Yan uwa kuwa kowa ya samu abin mata ko ya burgeshi sai ace *Asma'u!* Kowa sha'awar ta yake. Tin tana karama tayi mugun sabo da Aslam wanda in yaxo shi ke rainon ta gaba daya. Da anyi magana zaice *Asma'u* matar sa ce. Wannan yasa Dadyn *Asma'u* shaidawa zuri'ar su cewa ya bawa Aslam *Asma'u* ko yana da rai ko be da rai *Asma'u* ta Aslam ce. Aslam yaji dadin wannan hadin da akayi musu. haka ma Dadyn sa da Momyn sa. Inda sauran yan uwa masu son ta kowa ya janye kudurin sa yana sanya musu albarka Sam *Asma'u* bata san anyi ba dan a lokacin tana da karancin shekara bata san anyi ba. *ASLAM* Aslam saurayi ne dan shekara talatin kuma kwararen likita. Yana da katon asibitin sa wanda Mahaifin sa ya gina masa. Aslam yaro ne me farin jini, shima akwai fara'a da son yan uwan sa. Yan mata da yawa na son sa amman shi sam bai basu fuska. Dan yakan ce shi yana da *Husnah* sa kowa yasan sa da *Husnah* Daga cikin yan matan nashi ne ya hadu da preety wacce ta nace masa kuma tai wa kanta alkawarin duk daren dadewa sai ta aure shi. Aslam kyakyawa ne na karshe. Dan sai ka zata balarabe ne. wannan ya samo asali ne saboda, kakarsa dan yar libiya ce. Fari ne dogo jikin sa a murde dashi. Idanun sa manya, da siririn hanci sa da pink lips din sa. Duk jikin sa gashi ne kwance luf luf. Haka nan kansa suma ce cike a cikin ta. Wacce ita take karasawa ake ce masa balarabe. Aslam na son *Asma'u* sosai dan bai hada son ta da komai. Duk abinda zai faranta mata yana mata sai dai in yaga ba dai dai bane. Shi yake kara daura ta akan karatun ta dan ta waya zai mata bayanin duk abinda bata gane ba. Haka fanin addini ma duk takan tambaye shi koma meye dan ya riga da ya sabar mata. Dan ko wankan tsarki shi ya koyamata kafin ayi musu a isilamiyya. Haka wasu hukunce hukuncen duk yana sanar da ita dan babu kunya tana daukar sa tamkar Ya Buhari. Aslam shi ya hana a sanar da ita maganar bashi ita da akayi duk da yaga ta girma. Ya fadawa Dady kan a bari ya janyo hankalin ta tukunna. Dan haka bai dade da sanar da ita kudurin sa akanta ba. Lokacin da ya tare ta ba karamin nauyi abin yayi mata ba sai daga baya da kyar ta sanar masa ta amince. Amman duk son da yake mata in tayi masa laifi sai ya mata fada haka in koyar karatu ne ya tashi zasu ajiye batun soyayya a gefe. ya koya mata kome inda ya kamata ya koya mata. Haka in fanin soyayya ne ba a baya ba wajen fitar da duk abinda ke zuciyar sa ya fada mata Yasha fada mata. "Wallahi *Husnah* duk abinda nake fada miki wallahi daga cikin zuciyata yake ba koya ko kwafar na wasu nake ba. Abinda nake ji game dake, shi nake fada miki." Sosai yake mantar da ita duk damuwar ta da abinda yake damun ta ya faran ta mata. *Asma'u* kanji duk duniya ba wanda ya kai ta wajen samun soyayya. *INDABAWA* [1/18, 14:08] Maryam S Indabawa🥰:  *LABARIN RAYUWAR* *ASMA'U HUSNAH* BY *MARYAM S INDABAWA* *MANS* 🌐 *HAJWO* 🌐 *Hakuri da juriya Online writers*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 *Gidan Hakuri da juriya, tare da kawar da kai.* Facebook @ Indabawa Hausa Novel Wattpad @ Msindabawa instagram @ Maryam S Indabawa *31-35* DEDICATED TO *MAMAH NAH* Allah kara miki lafiya da imani yasa ki gama lafiya. *Ameen!* *Manzon Allah (SAW) Yace "Kuyi sahur domin a cikin sahur akwai albarka" Kamar ko yaushe tin asuba da ta tashi bata koma ba, bare yau da tasan suna da Sir Sabir. Da wuri ta sauka kasa ta gama duk abinda ya kamata tayi. Ta dawo dakin ta tayi wanka ta shafe jikin ta da mai. Durowar ta ta bude, ta tsaya kallon ta tayi minti Biyar a wajen sannan ta samu ta zaro wata bakar doguwar riga. Hannun rigar an masa irin dinkin babbar riga da wani yadin material me multicolour (Kaloli daban daban.) Sai gaban rigar da aka masa ado da stone (duwatsu) aka jere wasu manyan jajayen stone (duwatsu) guda takwas suma. Dago rigar tayi tana kare mata kallo, Ya Aslam ne ya siyo mata da yaje dubai. Juya ta ta kara yi, sannan ta dire akan gado. Wani jan skin tied ta dauko sai jar bra da pant, saka su tayi a jikin ta. Sannan ta dauko rigar ta saka ta daure ta, ta ciki. Jan hijab ta dauka wanda iya kar shi saman kirjin ta. Wani jan sandal ta dauko tasaka a kafar ta. Sai bakar jaka da ta zuba abin da take bukata. A kan gado ta ajiye jakar da wayar ta. Dakin Dady ta nufa, sai da yasa ta ci abinci sannan ya barta ya tafito. Jakar ta ta dauka, sannan wayar ta. Sakon Ya Haidar ta gani, budewa tayi tana murmushi. " *Assalamu Alaikum* Da fatan Baby na ta tashi lafiya, yasu Mami da Dady da Buhari. Ina fatan duk kuna lafiya. Daman zan fada miki ne ina kan hanyar Kaduna, ina bukatar addu'ar ki, in na isa zan kira dan nasan yanzu ba kya kusa." Murmushi tayi sannan ta nemi waje ta zauna. Sakon fatan alheri da isa lafiya tayi masa sannan ta tura masa. Ta jima tana tunani sannan ta tuna fa makaranta zata tafi. Da gudu ta fita tayi dakin yayan ta. Bacci sa yake kamar kullum, gadon ta fada. Da sauri ya mike, "Ya Salam!' Ya fada yana dafe kai. Murmushi ta saki, "Ina kwana yayanah." Harara ya wulla mata, ya mike ya shige ban daki. Zama tayi jiran sa. Wayar ta ce tayi kara, ta dauka. " *Asma'u* tara saura minti goma dai." Ido ta zaro waje tana mikewa, "Dan Allah da gaske," "Duba agogo ki gani." "Innalillahi wainna illahir rajiun. Gani nan gani nan." Ta fada tana nufar kofar ban dakin. "Yayah! Yayah!" Banza yayi mata. Kuka ta fashe masa dashi. "Yayah!" Ta fada cikin kukan. Shiru ya kara yi mata. Ya cigaba da cuda jikin sa. Sai da ya gama sannan ya dauro shawul ya fito. Tana jikin kofar a tsaye. Kallon ta yayi ya dauke kai ya fara goge jikin sa. Yana zama a gaban mudubi. Karasawa wajen sa tayi da sauri, ta durkusa akan gwiwo yin ta tace, "Yaya da Allah ka zo kakai ni makaranta na makara." Mai ya cigaba da shafawa. Kuka ta saka masa sosai. "Rufe min baki." ya fada fuskar sa a bace. "To Yaya dan Allah ka kaini makaranta." ta fada tana hade hannun ta gu daya. "Ina Baba da yake kai ki makaranta." tace, "Yaya na makara kuma Baba makara zamu yi dan baya gudu wallahi." "Ni ba inda zan kai ki." Kuka ta kuma saka masa. "To ya isa tashi bari nasa kaya. Toh ta fada tana fita, dakin Mami ta ttafi dan mata sallama. Kallo Mami ta bita dashi ganin idon ta yayi ja. "Me yasami idon ki, kuma daman baki tafi ba." Asma'u ta ce, "Yaya ne yasa ni kuka." Mami ta ce, "Akan me?" Tace, "Na makara yaki yazo ya kai ni." "Kin je tsokana har kika makara ko." "A'ah!" "Yanzu yana ina?" "Shiryawa yake, yanzu zai zo ya kaini." "Ok jeki same shi." Juyawa tayi, sai gashi nan ya shigo, cikin blue (ruwan omo) din shadda wacce akai mata aiki da dark blue, (ruwan omo me turuwa) blue hula yasaka, da bakin takalmi sai bakin agogo a daure a tsintsiyar hannun sa. Sosai yayi kyau, ya fito kamar wani tauraro, sai tashin kamshi yake. Durkusawa yayi har kasa. "Mami ina kwana. Da fatan an tashi lafiya?" "Lafiya lou. Ya ka tashi." "Lafiya Alhamdulilah! " "To jeka maza ka kaita makarantar daga nan ka wuce aiki zan aiki driver ya kawo maka abincin ka kaga ta makara." "To Mami sai na dawo." "Allah kiyaye hanya Allah muku Albarka." "Ameen!" Ya mike ya fice, komowa *Asma'u* tayi ta rumgume Mami ta mata kiss (sumbatar) a kumatu. Ta sake ta tana. 'Bye bye Mami." "Bye Ayi karatu sosai banda kula kawayen banza." "Insha Allahu." Ta fada tana fita a guje tana mata bye bye da hannu. Murmushi Mami tayi, dan *Asma'u* akwai ta da hankali ga nutsuwa, bar ta dai da tsokanar yayan ta amman komai nata cikin burgewa take yin sa. Baka ce *Asma'u* Kamar yadda Dady yake baki, shi kuma Ya Buhari fari ne ya dauko Mami. Amman komai na fuska da zubin jiki me kyau na Mami ne, dan Mami akwai diri hakan yasa ita ma *Asma'u* tana da diri me kyau. Kamar yadda shi kuma Ya Buhari ya dauko zubin jikin dadi dan dogune, sannan jikin su a murde yake, suna da dan jiki dai dai gwargwado. Bakin *Asma'u* bai mata muni ba sai kyau da ya kara mata. Dan Bakin ta me kyau ne, irin chocolate colour haka fatar ta take me kyau da taushi. Kowa na sha'awar kalar fatar ta. Kai ta jin jina. "Allah bada sa'a." ta fada a fili tana yin dakin Dady. Tana fita har ya shiga mota. Da gudu ta karasa ta bude gidan gaba ta shige. Hanya suka dauka. Cikin minti ashirin sun karasa makaranta. Har kofar department ya dire ta sannan ya juya. Tana karasawa kofar hall din su ta hange, sa a gaban aji. Sanye yake da ruwan madarar shadda wacce akai masa dinkin riga wacce da kadan ta wuce gwiwa da dogon wando. An masa aiki a jiki da dark brown (ruwan kasa) zare sai dark brown hula da takalmi dake kafar sa. Ta jima tana kallon sa, Sai bayani yake zuba musu. Daga bisani ta buya daga gefe dan kar ya ganta. Tinda ya mata kashe din kar ta matso masa kofar aaji muddin ta makara. Tana daga taga tana jiyo muryar sa, me sanyi da dadin sauraro. Sai da taga ya kusan fitowa sannan tabar kofar hall din. Ya fito ya tsaya a kofar ajin yana kallon ta, duk da ta bashi baya amman ya tabbata ita ce. Ya jima yana kallon ta ko zata juyo amman ina ko juyowa batai ba kamar tasan yana wajen. Wajen ya bari ya nufi Office din sa. Yana bawa wajen baya tana juyowa bayan sa ta tsaya kallo. Kai ta girgiza ta juyar da kanta. Zainab ce ta karaso wajen. "Sannun ki, kin kyauta." "Wallahi bansan lokaci ya tafi haka ba." "Haka dai kullum bayan kin gama tsokanar ki ko." "Ni yau ban tsokane sa ba." "Ke din kuwa." "Eh!" Dariya zainab tayi, "tashi ki rakani na siyo lemo dan Allah." Mikewa tayi suka nufi cafeteria. Sai da suka siyo lemo sannan suka dawo. Wajen da suka saba zama nan suka zauna gefen hall (dakinn daukar darasi) din su karkashi wata bishiya. Suna zama, sai ga kiran Ya Aslam nan. "Assalamu Alaikum!" "Wa'alaikum salam!" "Love!" "Na'am Yayana ya hanya?" "Hanya lafiya gashi har nagama komai yanzu sai gida, shine nace bari na karaso naga Queen of my heart." "Wow! Amman kuwa da ka kyauta." "Gani nan shigowa ckul din." "Sai ka karaso." "Aha." Ta kashe tana murmushi. "Waye zezo?" Zainab ta tambaye ya. "Ya Aslam ne." "Oh Allah kawo shi lafiya." "Ameen!" Yan department din sune suka karaso wajen su uku. Hafsat, Amina da Khadija. Bayan sun gaisa suka zauna. Hafsat sai hade fuska take Suna dan taba hira. Amman ita ta hade rai Zainab ce ta ce, " *Asma'u* wannan week end din zamu zo gidan ku, zamu kawo miki IV Fadila." "Eh daman ai ke bakya zuwa gidan mu sai da dalili wai ke kunya." Khadija ce, ta sa baki. "Ke zuwa kike." Murmushi Zainab tayi. "Yauwah tambayar min ita dai." Amina ce tace, "Yo ke ina ruwan ki. Sun fi kusa kuma kowa yasan zee bata son zumunci." Dariya Zainab tayi, "Ai ita tasan ina da zumunci tasan kuma me yasa yanzu na daina zuwa gidan su." Tsaki *Asma'u* tayi, "Wai fa dan Yaya Buhari saurayin tane shine fa." Khadija tace "To kunji dalilin ta ko." "Wannan ba dalili bane," Cewar Amina. "Yauwah yar uwa." *Asma'u* ta fada tana wa Zee gwalo. Zuwan wata katuwar mota shi yaja hankalin su banda *Asma'u* da tayi kasa da kai tana wasa da wayar ta. *Morning yan uwa ya kk ya gd da iyalai.* Pls don't forget to vote @Msindawa *MUJE ZUWA* *INDABAWA* [1/18, 14:09] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR*  ASMA'U HUSNAH BY *MARYAM S INDABAWA* *MANS* 🌐 *HAJWO* 🌐 *Hakuri da juriya Online writers*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 *Gidan Hakuri da juriya tare da kawar da kai, gidan zaman lafiya. Na gaida ku.* *36-40* Dedicated to My great *Mamah* Allah ya jikan ki ba dan kin mutu ba. Allah kara miki lafiya da nisan kwana mai albarka. Nagaida ke mahaifiya ta abar alfahari na. *Manzon Allah (SAW) ya ce, Idan zaka so mutum kada ka nuna masa tsananin so. in zaka kisa kada ka nuna masa tsananin ki. Dukkan su hankalin su ne yayi kan motar, banda *Asma'u* da ta daukar da kan ta, tana wasa da wayar ta. Khadija ce ta fara magana, ta ce, "Kai motar nan ta hadu amman." Amina tace, "Ai daga duk kan alamu, ma na cikin ta zai fi haka hauduwa." "Gaskiya kan motar ba karya, ko wane dan gayun ne a ciki." Hafsat ta fada "Ni kam ba ruwana da na ciki sai motar da ta burge ni." Zainab ta fada. "Kai Allah bani irin motar na." Hafsat ta fada. "Hassada kike yi tinda kika ce Allah baki irin ta sai dai kice Allah baki finta." Amina ta fada. "Duk karya ne irin haka nan, dan kaga Abu ka roki Allah yabaka irin sa shine haka." Zainab ta fada tana tabo *Asma'u* " *Asmy* kalli waccen motar amman tayi kyau wallahi." Kai ta dago ta kalli motar, ji tayi gaban ta ya fadi. "Eh tayi kyau." Ta fada tana mikewa sakamakon kiranta da ake yi. Can gefe ta koma jikin wata motar, ta dauki wayar. "Hallo my beauty! (Kyakyawa)" "Ya Aslam wannan ai tsokana ce." amsa ta amsa masa da muryar shagwaba. "Wacce tsokana nayi." ya tambaya "Wai beauty!" ta bashi amsa. "Oo Ke ba kyakyawar bace." Ya tambaya. Ta ce, "Gaskiya ni ba kyakyawa bace. Wannan ai sai kasa ayi min dariya." "Ba wanda zai miki dariya kinji, saboda kyan ki ba kowa ke da irin shi ba. Kina da wani kyau wanda kafin a samu mutum me irin sa ake dade wa. Ur skin is fresh with a beauty colour. (Fatar ki a murje, me kala me kyau)." Ta ce, "Uhmm please stop dis joking I beg you. (Dan Allah daina wannan tsokanar na roke ka." Murmushi yayi ya ce, "Wallahi I am not joking, I am telling the true. (Ba tsokanar ki nake ba ina fadan gaskiya ta ne.)" Baki ta turo ta ce, "Naji ya isa, ka karaso ne," "Eh! Gani kina ina ne." Ta ce, "Ina kofar department din mu," "Nima ina wajen." "Kai ya Aslam!" ta fada. "Da gaske ina wajen." "Ta ina." "Ina cikin wata Ash marsandi." "Oh na ganka. Ina ta bayan ka." "To kizo man." "A'ah Yaya please kai ka fito." "To gani nan." Baya ta juya masa. Kofar motar ya bude, wani sanyi da kamshi me dadi ne ya fito. Kafar sa ya ziro kasa. Safa ce da takalmi sau ciki bakake a kafar sa. Daya ya diro sannan ya fito gaba dayan sa. Suit ce a jikin sa, ruwan kumkumadi. Ya cire ta saman sai yar ciki da ya rage. Tin daga kafar sa na fara kallon sa inayin sama. har na karasa kirjin sa wanda yake a bude dashi na kirar cikaken namiji me jini a jiki wanda ya cika namiji. Kan fuskar sa na gangara. Fuskar sa me kyau ce doguwa fari ne tas dashi, sai manyan idanu wadan da suke a lumshe, wanda ake ce musu (sexy eye) Bakin shi dan karami ne, wanda yake da lebe me taushi gasu pink sai kwalli suke. Kansa cike yake da suma, kamar ta indiyawa. Sai saje dake gefen fuskar sa, wanda ya kara fito masa da kyaun fuskar sa. Idon sa sanye da farin gilashi. Masha Allah wannan gayen duk inda ake neman cikaken namiji me kyau da kwarjini ya kai ya ma wuce nan. Yan mata da yawa kallon sa suka tsaya yi sai gulmar sa akeyi. Dan ya gama haduwa ba karya. Waige waige ya farayi dan neman inda take, duk da ta juyar da kanta sai da ya gene ita ce. Dan duk jikin sa ya gama shaida masa, *Husnah* sa ce. Cikin tafiyar kasaita da nuna kalama tare da nutsuwa yake tafiya. Sannu a hankali har ya karasa gefen ta. Ta bayan ta ya zaro hannayen sa dake cikin alhiju ya rufe mata idanu. Jin an rufe mata ido da hannu me laushi, ga kamshin turare dake tashi, tasan Ya Aslam ne. Murmushi ta saki me sauti. "Haba My Hero, ai nasan kai ne." Hannun sa ya janye ya maidasu kan kafadun ta ya juyo da ita. Kasa magana yayi ya kure ta da idanu. Ido ta kashe masa guda daya. "Yah dai." Yawu ya hadiye tare da sauke ajiyar zuciya yana me sakin wani murmushi dake karawa fuskar sa kyau. Wani kallon soyayya yake aika mata dashi. Ba karamin kyau sukayi ba. "Baby nah kinyi kyau fa." ya fada yana kara kallon ta. "Zaka fara ko?" Ta fada tana nuna masa wasu kujeru da aka gina su. Zama yayi ita ma ta zauna. "Sannu Yaya nah Ya hanya?" ta tambaya cikin kulawa. Ya ce, "Hanya Alhamdulilah." "Sannu toh!" "Yauwah! Naji dadin zuwa na dana ganki Sweetheart, kin kara kyau, ashe duk hoton da nake gani rage min kyaun ki yake yi." "Yayana kenan yasu Momy." ta fada tana wasa da yatsun hannun ta. "Suna lafiya." Ya fada yaba dago face din ta. "Bari na karbo maka lemo." Ta mike. Kamo hannun ta yayi ya ce, "A'ah yanzu na gama cin abinci ga naku can ma a mota." Murmushi tayi, "Kai Yayah." "Eh!" "Zakaje gida ne." "A'ah! Daga nan zanyi gida." "Ok." "Ina sonki Baby nah." Murmushi tayi ta dukar da kanta. "Baby kunyar nan taki tana dada miki kyau." Kai ta kuma dukar wa. "Bari na wuce kar nayi dare. Tinda naga Baby nah ai nagodewa Allah." Murmushi tayi. "To nagode." "Nike da godiya Baby nah " Suka mike suka nufi motar. Dai dai karasowar Sir Sabir zai dauki motar sa. Kallon juna suka yi, ya shige motar sa. "Waye wancan." Juyawa tayi, "Sir Sabir wani lecturern mune." "Kuna magana ne?" Ya tambaya fuska a dan hade Kai ta girgiza ta ce, "A'ah!" "Ina zee kuwa?" Ya tambaya. Kallon gun da suke tayi ta ce, "Gata can bari na kira ta." Ta tafi wajen su Zee, "Zee kizo inji Ya Aslam!" Ta fada tana kamo hannun ta. Wajen su suka karasa. "A bamu waje ko?" Ya fada yana kallon *Asma'u* baki ta tabe ta bar wajen. Dariya yayi, yace, " *Husnah* rigima." Sannan ya dawo da hankalin sa kan Zee. Bayan sun gaisa yake bata amanar *Asma'u* sannan sukayi sallama. Wajen *Asma'u* yayi, "Haba Baby na yanzu da Yayan naki kike fushi. Kiyi hakuri kinji." Shiru tayi masa. Murmushi yayi, ya koma gaban ta, "Ko so kike na rumgume ki na rarashe ki." Ido ta zaro, tana girgiza kai. Ya jawo ta. Saurin janye hannu ta tayi. Tayi wajen motar sa. Bayan ta ya bi, yana Murmushi ya shiga motar. Leda ya miko mata. "Gashi ni zan tafi." Amsa tayi ta ce, "To Allah kiyaye hanya." "Ameen nagode!" Ta rufe masa kofar tana daga masa hannu. Tare da murmushi akan fuskar ta. Sai da taga bata hango shi sannan ta koma wajen kawayen ta. Ido suka bita dashi, " *Asma'u* waye wancan." Hafsat ta tambaya fuskar ta a hade. Kallon ta *Asma'u* tayi sannan ta dauke kai. Zainab ce, tace, "Yayan ta ne." Khadija tace, "Amman fa ya hadu. Wai meyasa ke kike baka ne." Amina ce, tace, "To ko zaki canja mata halitar ta ne," Harara ta Khadija tayi, "Ni na tambaye ta, ta wani haden rai da dauke kai." Hafsat ta fada, Mikewa *Asma'u* tayi ta kalle ta. "kin tambayen an amsa miki ba shikenan ba. ko kin manta wa kike tambaya ne. *Asma'u* da batai miki komai bace kika dau gabar duniya kika daura mata, kin manta in nayi miki magana ko kallo na bakya yi shine kuma yanzu zaki zo kina tambaya ta. Kuma cikin isa sai kace ni yar kice. Ke bama zan fada ba. Kiyi abinda xakiyi." Ta fada tana kama hannu Zainab suka shige hall. "Haba *Asma'u* me kenan kika yi ke da bakya fada." Kuka *Asma'u* ta fashe dashi, "Ya zanyi kema kinsan dai Hafsat ta kaini bango ne. Duk makarantan nan ba wacce ta tsana kamar ni tin ina dauke kai sannan yanzu tazo tana min gadara. Akan abinda be kai ya kawo ba." "Ya isah toh mene na kukan!" Ta fada tana jan ta jikin ta tana rarashin ta. Ta jima tana addu'a cikin ranta sannan taji sanyi. Kan ta, ta dago ta kalli Zainab. "Nagode besty." "Ba komai." kasa ta duka zata dauki jakar ta. Sai a lokacin ta tuna da abinda Ya Aslam ya kawo musu. Murmushi tayi ta dauki ledar tana dubawa. Takeaway yayi musu, guda uku sai dayar ledar kuma kaji ne guda biyu a ciki da lemuka na jarka. Raba su tayi gida biyu ta mikawa Zainab. "Besty dan Allah mikawa su Amina kayan nan." Karba tayi tayi waje. Su *Asma"u* na barin wajen, su Amina suka farayiwa Hafsat fada. "Haba Hafsat, meyasa kike haka, yarinya bata tsare miki komai ba amman kin tsane ta gaskiya ki daina haka." Hafsa ta ce, "Tayaya zakice bata taren komai ba, yarinyar da ta shigo ta same ni sannan tazo tafi ni kokari shine bata fini komai ba." Khadija ta ce, "Yo dan tafiki kokari, ai kema dagewa ya kamata kiyi ba ki tsane ta ba." Khadija ta fada tana bata fuska. "To ku dake ni mana." Hafsat ta fada. "A'ah A'ah ba abin duka anan. Sai dai muyi miki addu'a Allah ganar dake." Dai dai nan wata daliba da tayi kaurin suna a makarantar ta karaso gun su "Hae Babies." "Hae!" Gefen Hafsat ta zauna. "Dan Allah wa naga ta tsaya da yaron nan da yazo yanzu. Dan bayan ta na gani banga gaban ta ba." "Oh ai *Asma'u* Suleiman ce." Hafsat ta bata amsa. "Wane department take," Suka fada mata tai musu godiya ta bar wajen Zainab na fitowa Munasha na shiga Hall wajen *Asma'u* ta dosa kai tsaye, Toh masoya *Asma'u Husnah* naga sakon ku na gode, ba ma yan threestart u always love my story tnc Allah bar kauna. Hhhh yan facebook comment naku na min dadi ngd Afternoon yan uwa Don't forget to vote pls *INDABAWA* [1/18, 14:09] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* ASMA'U HUSNAH BY *MARYAM S INDABAWA* *MANS* 🌐 *HAJWO* 🌐 *Hakuri da juriya Online writers*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 Na gaida ku, yan 'kungiyar mu, Allah kara hade kan mu tare da dada mana hakuri da juriya da al umma. Hajiya Nafisa na gaida ki. Allah kara daukaka Ameen. Mamanah. *41-45* Dedicated to *My sweet Mum* Allah kara miki imani da daukaka. An Ruwaito Cikin Littafin Ibn Sinni, Daga *Buraidah (ra)* Yace: *Manzon Allah(ﷺ)* Yace: "Duk Wanda Yayi Wannan Addu'ar a Yayin da ya Wayi Gari da Kuma Lokacin da Yayi Yammaci, *{Rrabbiyallahu Tawakkaltu Alaihi La'ilaha Illah Huwa Alaihi Tawakkaltu wa Huwa Rabbul Arshil Azeeem, Lã'ilaha Illallahu Aliyul Azeem, Mãsha Allahu Kana, Wama Lam Yasha Lam Yakun, A'alamu Annallaha Ala Kulli Shai'in Qadeer, Wa Annallaha Qad Ahad'a Bi Kulli Shai'in Ilma},* Sannan Ya Mutu Zai Shiga Aljanna Tana karasawa wajen, tace, "Hae Bae!" Murmushi *Asma'u* tayi. "Sannu!" "Yauwah! Uhmm daman nace wanda yazo din nan sunan sa nake son ji." Murmushi *Asma'u* tayi, "Ya Aslam Sunan sa." "Ok toh nagode." Ta fada tana mikewa dai dai karasowar Zainab. Kallo Zainab tabi ta dashi, ta karasa gun *Asma'u* Fuskar ta a daure take tambayar ta. "Me ya hada ki da waccan?" Bin ta *Asma'u* tayi da kallo. "Tambayata tayi." "Akan wa?" "Ya Aslam mana." " *Asma'u* kin san wace wannan kuwa?" ido Asma'u ta bude alamar tsoro. Ta girgiza kai ta ce, "A'ah wace?" "Toh! Ita ce wacce ake kira Munasha! Kinsan dai Munasha ita ce wacce ba abinda bata aikatawa, ki kula da ita dai." Ido *Asma'u* ta zaro, saboda tsoro. "Wallahi ban sani ba." "Ki dai kula." "Insha Allahu." Daga nan suka fara cin abinci, suna gamawa aka fara taruwa a hall din. Gaba suka koma, sai ga lecturer su nan. Sai karfe hudu ya fita, sallah sukayi suka shige library dan yin karatu. "Sis Koyan lecture da Sir Sabir yayi muku yau." Asma'u ta fadawa zee "Toh!" Ta fada tana koya mata, sosai take ganewa. Sai karfe biyar da rabi sannan suka fito, lokacin har anzo dibar su. Sallama sukayi, suka wuce. Tana komawa gida ta tadda Mamin ta a falo. Kanta ta haye, "Mami na ya gida?" "Lafiya Alhamdulilah, Ya makarantar?" "Lafiya Mami." "Tashi kije kici abinci nasan baki ci komai ba." "Lah Mami naci Abinci. Mami kinga yau Ya Aslam ma yazo makarantar mu." Ta fada tana murmushi, fuska Mami ta dan hade, ta ce "Wajen wa yaje?" "Wucewa zai yi ya biyo." Asma'u ta bata amsa. " *Asma'u* ban yadda ki kara bari ya same ki a makaranta ba, ke bashi ba koma waye kar ki kuma haduwa da wani namiji a makaranta." Fuska ta marairaice, "Mami dan Allah kiyi hakuri, bazan kara ba." "Ba komai baki bata min ba. Amman kika kuma shi zai batan rai." "Kiyi hakuri insha Allahu bazan kuma ba." "Kar ki damu tashi kije ki rage kayan jikin ki." "Kin hakura toh!" asma'u ta tambayi Mami. Murmushi Mami tayi, " *Asma'u* kenan. Na hakura, kinji." Murmushi tayi ta tashi ta haye sama. Murmushi Mami ta kuma yi, tana girgiza kai, *Asma'u* sam bata son bacin ran iyayen ta ko ya tayi musu laifi zata daga hankalin ta, har sai taga sun hakura. Ita kanta Mami tasan ba wani abu bane dan Aslam yaje makarantar ba, amman in har bata tsawa tar ba nan gaba zata iya bawa kowa damar yin haka. kuma hakan baya da kyau. Tana shiga dakin ta ta fara lalubar number sa. Bugu daya ya daga. "Yayanah ya hanya?" "Hanya lafiya Alhamdulilah na kusa karasawa." "Kai Yaya gudu kake yi ko?" "So nake nayi sauri na karasa." "Dan Allah ka rage gudun nan." "To shikenan sai anjima." "Aha! Ka kula da kan ka." "Insha Allah!" Ta kashe wayar tana sauke ajiyar zuciya ne. Bandaki ta shiga tayi wanka sannan ta fito. Kwalliya tayi me kyau, ta saka riga da siket yan kanti ruwan madara da dark brown. Brown (Ruwan kasa) din hijab ta dauka ta saka sanna ta dauko jakar ta tana duba wa. Tana gama dubawa ta mike ta hau kan sallaya, tana jan carbi. Kiran sallah da taji ya sanya ta mike ta tada sallah. Tana idar wa ta janyo Alkur'anin ta, tana karantawa. sai da akayi sallah isha'i sannan ta mike tayo. Tayi Isha'i sannan, ta mike tayi shafa'i da wuturi. Tana idar wa ta fara yin addu'a. Wayar tace tayi kara dubawa tayi. Sakon Ya Aslam ne ya shigo. *Baby nah, na sauka lafiya. Zan kira ki anjima.* Murmushi tayi, ta mike tayi waje. Tinda ya gansu a tsaye ya kasa sukuni sam ya kasa samun nustsuwa, waye wannan da yazo gun ta, sam shi abin damun sa yake. Haka ranar ya gama, aiki duk jikin sa babu dadi, ransa a bace dan abin be masa dadi ba. Haka ya tashi a aiki ya wuce gida. Mamah na gani sa taji hankalin ta ya tashi, dan duk ya fita a haiyacin sa. Gaishe ta yayi, ta amsa. "Sabir lafiya kuwa?" "Lafiya lou Mamah." Kallon sa tayi, tana me girgixa kan ta. "Wai Sabir mecece ni a gunka." Kan sa ya dago, yana kallon ta. "Eh! Tambayar ka nayi," "Mamah Mahaifiya tace ke." "Ka tabbata?." "Na tabbata Mamah." "Amman kuma me yasa in zurfin cikin naka ya tashi har ni da nake mahaifiyar ka, kake boye min." Kai ya sunkuyar, "Mamah kiyi hakuri." "Ni kawai ka fada me ke damun ka." "Mamah ni ba abinda ke damuna aiki ne kawai." "Shikenan Sabir, tinda haka ka zaba ai shikenan. Nidai zan ta tayaka da addu'a Allah ya, yaye maka abinda ke damun ka." "Ameen! Mamah nagode Allah kara girma." "Ameen! Abincin fa zaka ci yanzu ko sai anjima?" "Mamah ban dade daci ba, sai dai in anjima." "To shikenan." Ya mike yayi dakin sa. Kanta ta girgiza tana jinjina zurfin cikin Sabir da ko ita, bazai fadawa damuwar sa ba. Ta dauki a niyyar sashi a addu'a Allah ya yaye masa koma me ke damun sa. Sabir dan gidan, Alhaji Marzuk ne, da matar sa firdausi, yana aiki a ma'aikatar lafiya ne dake jigawa. Inda ita kuma matar sa ke aiki a ma'aikatar ilimi. yayan su uku. Biyu mata daya namiji. Rukkaya ita ce babba wacce, tayi aure a Lagos ya'yan ta uku. Maza biyu daya mace Maryam Sai me bi mata, Mufidda wacce take, aure a nan kano. Ya'yan ta biyu. Sai Auta Sabir, wanda yake babban likita a nan asibitin Aminu kano. Yanzu haka an dauki contract ne inda yake lecturing. Mahaifin Sabir na son Sabir haka ma maman sa da yan uwan sa. Basu da buri sai na suga yayi aure. Mamah sa tayi, tayi yayi aure yace lokaci ne beyi ba. Ba kalar matan da bata kawo masa ba amman sam ko kallo bai isar sa. Dan yanzu haka ta bashi lokaci indai bai yadda ba zata hada shi da koma waye. Zaune suke, da kwalbar giya a gaban su. Wacece in ba Munasha da Bilkis ba. Aminan juna wanda harkar su take iri daya kuma hali ma iri daya wannan ya kara hada aminan takar tasu. "Munasha, Jibson ya kawo karar ki, wai kin ki ki bashi hadin kai." Fuska Munasha ta hade, tare da zukar tabar dake hannun ta. "Bilkis Amman na fada miki, cewar tin ranar da na hadu da yaron nan duk kan bukata ta da sha'awa ta, ta koma kansa." "Amman dai nasan kina shan azaba dan kin saba da rayuwa da maza, yanzu nasan kina cikin tashin hankali." Idanun ta ta dago wadan da suke jijir dasu. "Haka ne, amman zuciyata ta, tafi wajen wani can." "Ki daure kije gare shi ko kya samu nutsuwa." "Kina ganin beyi zuciya ba." "Tayya zaiyi zuciya dake bayan yasan matsayin ki da irin zumar da kike shayar dashi." Ido ta juya, "Amman kice lalashi na kika yi." "Daman mana." "Ok jeki." Ta mike tayi benen wajen. Kwabar da ke gaban ta ta dauka ta zuba giyar dake ciki a kofi. Sha ta farayi, tana lumshe ido sai kace me shan wani abin dadi. *Wacece Munasha* Munasha, suna ta na ainihi Maimuna, mahaifin ta Malam Anas, Sai Mahifiyar su Sadiya. talakawane dan mahaifin ta itace yake siyar wa. Basa dai taba rasa abinda zasu ci, haka nan sutura duk shekara yana dinka musu ita kala biyu ko daya. Mahaifiyar ta aikato take yi a wani gida dake unguwar su, anan take samar musu yan kwancen kaya, da dan abinci. Munasha, ta kasance me kwadayi da son abun duniya. Duk kokarin da Mahaifin ta yayi mata, abu bata taba ganin ya mata sai rainuwa haka nan abinci, in anyi shima sai ta ga damar ci. Ya sanya su a makarantar boko da arabi. Bokon dai dayaya aka gama ta. Hakan yasa tana yin candy ta fara bin maza. Dan a duniya tana son ta ganta da kudi wannan yasa, ta fara bin maza. Ganin mahaifin ta zai hana ta fita yasa a cikin Yan iskan su, tasa wani yazo, a zuwan ya dauki nauyin karatun ta. Mahaifin Munasha yaji dadi da wannan abin wannan yasa Munasha ta samu kafar fita. Dan wani lokacin ma haka tace ta koma hostel da zama. Nan kuwa ba a hostel din da take in ba club ba sai, sai gidan samarin ta. Munasha, ta zama babba a harkar karuwanci, muje zuwa dan cigana da jin lbrin Munasha. *INDABAWA* [1/18, 14:09] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR*  ASMA'U HUSNAH BY *MARYAM S INDABAWA* *MANS* 🌐 *HAJWO* 🌐 *Hakuri da juriya Online writers*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 *46-50* Dedicated to my love mother. *Momy nah* Really love u An Ruwaito Cikin Littafin Ibn Sinni, Daga *Anas (ra)* Lallai *Manzon Allah(ﷺ)* Yace: "Shin 'Dayanku Zai Gajiya Ya Zamo Kamar Abi-Damdama?" Sai Sahabbai Sukace Wanene Abu-Damdama Ya Annabin Allah? Sai Yace: Ya Kasance Idan Ya Wayi Gari Yana Cewa: *{Allãhumma Inni Qad Wahabtu Nafsi Wa Irdi Laka, Falã Yashtumu Man Shatamahu, Wala Yazlimu Man Zalamahu, Wwala Yadribu Man Darabahu}* *KARASHEN LBRN Munasha* A cikin kawayen ta mutum daya ce ta arxiki. Wacce tun fara bin mazan ta take mata fada akan irin samarin da take kulawa. Dan ke daga ganin samarin ma xaka san yan iska ne, bare in suna mu'amala suyi ta taba ta. Ko ace za'a tafa. Ko in tana bukatar abu sai dai tace saurayi yayi mata. Rashida yar gidan masu hali ce, dan sau tari takan bata kudi kashe wa. Sannan in an mata kaya kala uku zata dau daya ta bata. Amman sam Maimuna bata godewa Allah. Ita burin ta tagan ta ta kula me kudi wanda zai na kashe mata kudi. Bayan yawancin samarin yanzu basa yin abu dan Allah sai dai in zasu fansha. Rashida takan mata fada. "Haba Maimuna, yanzu da hankalin ki, kike kula wadan nan mazan. Shin me yan mata memukeso muzamane, ina hankalin mu yake ina tunanin muyake ne, Shin iyayen mu me suka gaza yimana muke nema mudorawa kan mu akan hanyar da baza ta bulle da mu bane. Duk kokarin da Baba yake, amman kike son daurawa saurayi duk buqatar ki. Haba yar uwata ashe kinyadda saurayinki xemiki abunda iyayenki baxasu yimiki, Maimuna ki nemo hankalinki da nutsuwar ki6oye son abun duniyarki badon komaiba sedan kitsira da martabarki taki ta 'ya mace. saurayi nagaskiya shine wanda yake sonki da aure baya neman komai daga gareki burinsa yaga kin tsira da mutuncinki. Saurayi mayaudari shine Wanda yake miki hidima ba don Allah ba sedan kibashi gishiri yabaki manda. Mace wadda akasanta da kunya, tarbiyya, mutunci, Jan aji, kamala, sanin yakamata, amman kin manta dacewa yanxu xamani yasanja wasu daga cikin samari sundena abu dan Allah sedan samun riba. wallahi Maimuna, idan saurayi yafuskanci ke kinada kwadayi akwai matsala ta hanyar haka xesamu damar isar da qudurinsa, wallhi saurayi bashida abun duniyar daxe rudeki yaxubar miki da mutuncinki bashida abunda xemiki wanda iyayenki xasukasa. Alokacin bakida damar hanashi duk abinda yanema domin shi kika fara mora. kinsan ko farce yata6a miki yacuceki dan Allah Mainuna ki kula." Duk lokacin da Rashida tai mata fada takan dauka. Amman da ta hadu da yan harkar ta zata manta. In kuma Rashida tai musu fada gaba dayan su, sai suce dan ita Rashida din yar masu Hali ce shi yasa bata san halin da suke ciki ba. Tin asali Yayan Rashida ke son Maimuna, amman tafiyar sa karatu malesia, shi ya sa soyayar ta ja baya. Duk da a cikin zuciyar sa bai da burin da ya wuce ya kamala karatu ya dawo ya tai maki rayuwar Maimuna da mahaifin ta ba. Itama a zuciyar ta shi take so, dan Nasir namiji ne wanda ya amsa sunan namiji, ya hada komai kyau ilimi da gayu. tinda ya tafi be dawo ba duk da suna waya amman karatu yana dauke hankalin sa. Ba dan baya son ta yafi bawa karatu lokacin sa ba. A'ah sai dan son da yake yaga ya kammala karatun sa ya fito da sakamako me kyau. Maimuna kyakyawa ce ajin karshe, fara me kyaun sura. Amman duk ta zubar da mutuncin ta. Har Kungiya ce, da ita wace take daukar yara ta kaisu wajen manyan Alhazai. Wanda har a cikin makaranta ma, akwai wadan da suka daure mata gindi. Yanzu haka Munasha ta zama kwarariya dan ta kama naira a hannu. Yanzu haka da taga saurayi yayi mata zata san yadda zatayi ta ja hankalin sa. Har wajen malamai take kai mutum a janyo mata hankalin sa. Munasha babbar yar duniya ce wcce idon ta ya gama budewa. Ba kasar da bata fita. A harkar karuwanci dai ta fita zakkah. Amman duk da haka, son Nasir na cikin ranta. *-*-*-*-*-*-*-*-* Kwance take a kan gadon ta, sanye take da hijab fuskar ta, tayi kyau da ita. Sai futar da annuri take, allon wayar take kallo. Wannan yasa na mika kai dan ganin abinda take yi. Aslam na gano kwance akan katon gadon sa, yana sanye da blue (ruwan omo) din T-shirt, da blue din wando, da alamar kayan bacci ne a jikin sa. Magana ya ke fada mata kunne na kasa ina sauraro. "Ke na bawa zuciyata *Asma'u*, ki adanata dan nasan zaki mata gata," Murmushi *Asma'u* keyi. Sanna tace, "Hmm Ya Aslam. Gakiya kam zan kula maka da ita fiye da yadda zan kula da tawa." "Nima na sani. na baki ita ne saboda bana son kowa ya taba ta. Duk wanda zai shiga ke zaki bashi izinin shigar ta" Murmushi tayi. Ya cigaba da magana "Dake na fiso muyi soyayya, sannan dake nafi son muyi rayuwa. Dan Banda kamar ki a duniya, wannan yasa na mallaka miki zuciya ta" "Kai Ya Aslam!" Ido ya kanne mata ya ce, "Ke ta daban ce. Shi yasa kullum yabon ki nake. Ke nake son ki kasance a kusa dani. Dan kece kadai farin ciki na." Shiru *Asma'u* tayi tana sauraron sa, tare da lumshe idanun ta. Kallon kyakyawar fuskar ta yake yi. "Ke ce Taurruwa ta. ke kika hasken zuciyata. Kin kawar min da dukkan damuwa ta. Ban da bakin magana gare ki ban san irin godiya da zan miki ba. Ban san kuma me kike son na miki ba." Idon ta, *Asma'u* ta bude, ta kira sunan sa. "Ya Aslam!" Kallon ta yayi kafin ya amsa da "Na'am Baby nah!" Ta ce, "Alkawari nake son karike min koman wuya kar mu rabu kaji." Murmushi yayi, ya gyara kwanciyar sa. Yana kara fuskan tar ta. "Alkawari na rike miki kuma koman wuya bazan rabu dake ba kinji." "Nagode!" Kallon ta yayi yana kashe mata idanu kamar me jin bacci. Kasa tayi da kanta. "Wallahi rabuwar mu abu ce me wuya dan mun zama hanta da jini. Ko 'da da uwa." Dariya ta saka tana girgiza kanta. Shima dariyar yake. "Wallahi da gaske nake. Na fada miki duk abinda kika ji na fada daga zuciyata yake. Abinda zuciya ta take ji kenan baki na ya furta miki." "Na yadda da kai Yayanah. a zuciya ban da kamar ka komai nawa ya zama naka. Amman dan Allah kar ka yadani ka kula da soyayya ta. Dan kai dai na aminta dakai kuma na yadda da kai. Mun shaku mun saba Ya Aslam abin da ya rage kawai auren mu ne." Ta fada yana rufe fuskar ta da tafukan hannayen ta. "Oo please kicire kunyar nan cigaba da narka min zuciya mana." Ido ta zaro "tayaya zan cigaba da narka maka zuciya. Yanzu ya zanyi in na narka maka zuciya." "Sai muyi amfani da taki ko?" "A'ah muyi amfani da taka dai." "To cigaba ina jinki." "Kai Ya Aslam" Kunnen sa ya kama yace, "Yana jira zai kaiwa zuciyar ki abinci taci." Dariya ta saki. "Ya Aslam kenan!" "Allah yunwa take ji fa." "Toh Zan kasance me share maka hawaye a duk lokacin da zasu zuba zan hana su zuba. Zan kyautata maka in faran ta maka." "Allah tabbatar mana da Alheri, sannan nikai na bazan taba barin ki kiyi kuka ba." "Nagode!" "Ba godiya a tsakanin mu." Murmushi sukayi gaba dayan su. "Tashi kije kiyi Alwala kizo kiyi addu'ar bacci." "Toh!" Ta fada tana tashi. Ban daki taje tayo alwala. Addu'a tayi, yana jin ta har ta gama. Wayar ya kashe, sannan ya kirata. Kamar yadda ya saba yi mata kissa Annabawa haka ya farayo mata har bacci ya dauke ta. Washe gari ya kama asabar dan haka tin da ta tashi da asuba tayi sallah. Ta fara gyara dakin ta, tin daga karkashin gado har su durowar ta duk da ba datti amman sai da ta gyare ta goge ko ina. Sannan ta fita madafin su (kitchen) ba kowa a ciki wannan ya tabbatar mata da Mami na can gyaran daki. Dan duk karshen sati sai sun gyare gida ko ina da ina tsab. Wake ta auna tayi waje dashi. Ban garen masu aiki tayi. Baba Lami ta sama zaune. Gaishe ta tayi, sannan ta tambaya ko Lubabatu na nan. Kiran ta Baba Lami tayi. Lubabatu na ganin *Asam'u* ta saki murmushi. "Ina kwana?" "Lafiya lou." "Dan Allah daman waken nan zaki surfa min saboda kar na makara zan je isilamiyya." "Bakomai kawo." Ta mika mata. Ta juya ta fita. Kunun gyada ta dama musu, sannan ta hau gyaran kitchen din nasu. Sai da tagama gyara sannan Lubabatu ta kawo mata markaden. Kayan hadi ta zuba sannan ta fara soya kosai. Kosan kuwa yayi kyau dashi ya tashi abin sha'awa. Tana gamawa ta gyara falon su, sannan ta jere kayan karin nasu a inda suke cin abinci. Kitchen din ta gyara ta wanke duk abinda ta bata. Dakin ta ta koma tayi wanka sannan ta shirya cikin riga da siket yan kanti. Sai ruwan tokar hijab da ta dau wanda yake a wanke a goge dashi. Dakin Dady tayi, ta gaishe dashi sannan suka sauko kasa, Mami ce ta sauko da Ya Buhari, suka gaisa. Sannan suka fara karya wa. Suna gamawa ta mike ta haye sama. Hijab din ta! Ta saka wanda yake har kasa. Sai nikaf da ta saka kafar ta da safa. Jakar ta ta dauka, ta fito. "Mami da Dady na tafi sai na dawo." "To a dawo lafiya Allah bada sa'a" "Ameen!" Ta fice. Yan uwa ya daren? Toh sai Allah ya kaimi gobe in muna da rai da lafiya. Nagode *INDABAWA*: [1/18, 14:10] Maryam S Indabawa🥰:  *LABARIN RAYUWAR* ASMA'U HUSNAH By *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* DEDICATED TO *MY UMMU NAH* *Ummah farin cikin zuciyata. abar alfahari na.* *51-55* An Ruwaito Daga Cikinsa, Daga *Abi-Darda'i (ra)* Daga *Annabi (ﷺ)* Yace: "Duk Wanda Yace a Kowane Rana Yayin da ya Wayi Gari da Kuma Lokacin da Yayi Yammaci: *{Hasbiyallahu Lã'ilaha Illah Huwa Alaihi Tawakkaltu Wa Huwa Rabbul Arshil Azeem}³*, Sau Bakwai, Allah Zai Isan Masa ga Dukkan Damuwarsa ta Duniya da Lahira"._ ________________________ Asma'u sai sha biyu da rabi ta dawo. a gajiye ta dawo ga rana. Tana shigowa gida Mami ta tare tana "oyoyo 'yar ta" Murmushi tayi ta karasa gun Mamin ta, ta zauna a gefen ta. ta ce, "Mami sannu da gida!" "Yauwah Asma'u ya makarantar?" Asma'u ta ce, "Lafiya Alhamdulillah!" Mikewa tayi ta ce, "Mami bari naje na watsa ruwa." "Toh!" Tayi sama, tana shiga ta ajiye jakar ta, ta cire kayan ta ta sakale su ta shiga bandaki. Ta jima tana watsa ruwa sai da taji sanyi sannan ta cuda jikin ta. Tana fitowa ta saka wata doguwar riga mara hannu. Hijab ta saka ta tada sallah. Sai da ta idar sannan ta shafa mai ta shafa hoda. Wayar ta dake ta kara tin tana bandaki ta dauka. Yaa Aslam ne dan haka da sauri ta dauki wayar ta kara akunnen ta. Sai da yai sallama ta amsa sannan ya tambaye ta ya makaranta. Dan yanzu ya kira Mami ta ce yanzu ta dawo. Da wayar a kunnen ta, ta sauka kasa dan samar abu me sanyi. Ice cream ta dauko a firij din dake kitchen din su, sannan ta dawo falo inda Mami take. Wayar ta kashe tana kallan Mami ta ce, "Mami Zafi bai yiba wallahi." Mami ta ce, "Ranar da kika kwaso ce kinsan sha biyu lokacin tafi budewa." Ice cream din ta fara sha tana lumshe ido har ta EMgama ta kwanta. Ta ce, "Mami bari na dan yi bacci kafin anjima dan nagaji." Mami ta ce, "Ai gara kina huta wa." Cikin kankanin lokaci bacci ya dauke ta. Mami na zaune a gefen ta, ta zuba mata ido. Mami bata san saboda me ba. Amman Asma'u na yawan bata tausayi. Yanzu da tana baccin ma kallon ta kawai take tana dada jin kaunar 'yar tata. Asma'u ba dai hazaka ba sam ina ta tashi tin safe sai goman dare zata kwata. In kuma ta tashi da asuba bata kara rintsawa ga karatun su mai wahala. Amman kuma komai nata yana tafiya dai dai. Sai dai wani lokacin in karatu ya sako ta a gaba har ramewa take yi dan ko lokacin cin abinci bata samu. Kafin la'asar ta tashi tayi sallah sannan ta dawo falo ta zauna tana danyin chatting a wayar ta. Tana zaune taji sallamar Zainab da gudu ta mike tana rungume ta. "Ah lallai yau Zee ce a gidan namu." Hararar ta Zainab tayi ta ce, "Ke dallah a gaban Mamin." Ta dan daura mata hannu akan leben ta. "Mami na kitchen bari na kirata ku gaisa mu tafi sama zaki fi sakewa." Hanyar kitchen tayi tana kwadawa Mami kira. Mami ta fito ta ce, "Lafiya?" Asma'u ta ce, "Mami, Zainab ce ta zo." "Allah sarki sannun ta da zuwa ina zuwa." Ta koma kitchen din ta rage gas sannan ta fito. A falo ta same su. Zainab na ganin Mami ta sauka daga kan kujera tai kasa da kai tana gaishe da Mami cikin girma mawa. Mami na tambayar ta su Maman ta. Sai da suka gaisa Mami ta koma kitchen sannan suka koma sama. Suna zama yar aikin su Asma'u ta kawo mata ruwa da lemo hadi da snacks. Suna hira tana ci har basu san magariba tayi ba sai kiran sallah da sukaji kawai. Ido Zainab tayo waje dasu ta ce, "Nashiga uku salar me?" Dariya Asma'u tayi ta ce, "Mene magariba ce." Duka takai mata ta ce, "Shine kike min dariya ko?" "Sorry ta tashi muyi sallah ko?" Ta mike ta shige ban daki alwala tayi sannan ta fito ta tada sallah. Asma'u ma bandaki ta shiga tayo alwala tai sallah. Suna idar wa Zainab ta mike. Kallon ta Asma'u tayi ta ce, "Ai kya bari dai kici abinci Yaya ya dawo mukai ki gida ko?" "Rufan asiri dare ai sai ya karayi." Hararar ta Asma'u tayi ta ce, "Da yake a jeji kike ko? To in na fadawa Momin taki ana zaki kwana fa." Dariya Zainab tayi ta dauki jakar ta ce, "Ni tashi muje." "Allah sai kinci abinci." Ta fada tana fita daga dakin. Kitchen ta shiga ta hado mata abincin da sukai. Tuwon semo ne miyar agushi taji nama sai kamshi take. Sai lemon ginger da Mami ta hada musu. Diba tayi a babban faranti tayi daki dashi. A zaune ta tadda Zainab tana shiga Zainab ta amshi kayan ta dire ta fara zubawa dan tai sauri ta gama su tafi. Sai da taci ta koshi sannan ta mike ta wanke hannu. Kiran sallah isha'i taji wannan yasa tana fitowa ta tada sallah. Tana idar wa kuwa ta mike tayi waje. Asma'u tabi bayan ta tana cewa, "Ai kya bari nayiwa Mami magana ko?" Tsayawa tayi ta na kallon Asma'u, kallon ta Asma'u tayi ta ce, "Ga kujera ki zauna man." Zama tayi ita kuma ta shige dakin Mami. Mami na zaune tayi kwalliya kamar yadda ta saba ta tarbar Dady. "Mami zata tafi!" "Au har ta fito." "Eh!" Asma'u ta bata amsa. Leda Mami ta nuna mata ta ce, "Dauki wacan ki kai mata ki dauki dubu biyu, ki bata kisa Baba ya kai ku ki rakata." "To Mami Allah kara budi da girma." "Ameen muje nai mata sallama ko?" Suka fita tare Asma'u rike da ledar kayan kwalliya a hannun ta. Sai da Mami tai mata sallama tare da godiya, sannan suka fita tare da Asma'u. Suna fita suka tadda Yaa Buhari ya dawo. Asma'u ta ce, "Yauwah kinga Yaya ya kaiki ma ko?" Banza Zainab tai mata har suka karasa gefen sa. Murmushi yake sakarwa Zainab dan shi bai ma kula da wata Asma'u ba. Asma'u dake gefe ta ce, "Ah lallai soyayya!" Duka ya kai mata. Tai sauri kaucewa. Tana dariya. "Kaga Yaya muje ka kaimu dare nayi." Gaba yayi Zainab tabi bayan ta shi ya bude mata mazaunin ta gaba ta shiga. Asma'u ta tsaya ta ce, "Ai kuwa nima sai an bude min in ba haka ba bazan raka ku ba." Rankwashi Yai mata ya ce, "In na bude me zai cijeni." "Babu!" Asma'u ta fada tana zama a cikin motar. Suna tafe suna hira suka bar Asma'u ganin haka yasa ta dauko waya ta kira Yaa Aslam. Waya suke tana bashi labarin zuwan Zainab da abinda suke mata. Hakuri ya bata ya ce, "Dadin ta kema kina da wanda zaki hirar dashi ko?" "Eh man." Daga nan suka dinga waya har aka zo gidan su Zainab. Sai da Asma'u ta rakata gida ta gaida Momin ta sannan sukai sallama Momi na mata godiyar kayan da Mami ta bata. A mota ma wayar ta taci gaba dayi tabar Yaa Buhari yana ta surutun sa shi kadai. Sai da ta gama waya da take yai ta mita ta ce, "Kaji Yaya kai lokacin da kukai min banza me nace nima ramawa zanyi." Dariya yayi ya ce, "Wai wane wannan sirikin nawa ne?" "Bazan fada ba." Dariya yayi ya ce "kinsan dai dole na sani ko?" "Naji lokacin ka sani." Daga haka suka cigaba da hirar su abin sha'awa har suka koma gida. A falo suka tadda Dady suka masa sannu da zuwa sannan ssuka ci abinci. Sannan kowa yayi daki sa dan yin bacci. Kamar yadda ta saba haka tana kwanciyya Yaa Aslam ya kira. Sai da sukai waya sannan sukai awala tai addu'a suka kwanta yana mata tarihin sahaban mazon Allah (SAW) *Indabawa* [1/18, 14:11] Maryam S Indabawa🥰:  *LABARIN E RAYUWAR* ASMA'U HUSNAH By *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* Dedicated to *My Mommah* *Uwata gari mai burin ganun cugaba da ingantuwar tarbiyyar ya'yan ta.* Na gauda duk wata *UWA* Allah kuma yai muku kyakyawan karshe ya bamu ikon muku biyayya yasa mu gama daku lafiya. *56-60* *Wanda kame harshensa, ya kiyaye farjinsa, ya shiga taitayinsa, ba zai ta6a yin Danasani a Duniya ba.* Yau kamar kullum tin asuba bata koma bacci ba sai da ta gama komai tayi wanka sannan ta shirya cikin jar doguwar riga mai dogon hannu. Sai bakin mayafi da ta yafa. Bakar jaka ta dauko ta ciro littafan ta ta zuba a ciki. Turare ta fesa ta dauki bakin cover shoe ta saka ta tafi dan yiwa Dady sallama. Dady ya amsa yana kallon ta ya saki murmushi ya ce, " *Husnah* kinyi kyau!" Murmushi tayi ta zauna suka gaisa, anan yake fada mata ginin asibitin da ake mata ya kammalu dan haka zai je yayo order kayan da za'a zuba. Asma'u baki yaki rufowa sai murmushi take tana ta godiya ga Dady. Ba abinda Dady yake so kamar yaga ya farantawa iyalan sa. Hannun ta ya kamo ya ce, " *Husnah* ki kara gwazo ba abinda bazan miki ba in dai bai fi karfi na ba kome ne indai kina so zan miki." Murmushi tayi ta ce, "Dady nagode!" Abinci ta hada masa, kallon ta yayi nan da nan ta gane abinda yake nufi dan haka ta fara hada tea. Agogo ta kalla taga har karfe takwas tayi. Yau za'ai submitting assignmenat din Sir Sabir gashi ya ce in takwas da rabi tayi monitor yakai masa. Tana rasa dalilin da yake sata tana yawan makara. Ba yadda zatai yiwa Dady haka ta zauna ta dinga cusa abinci har ta gama ta mike. Kudi ya bata ta amsa tana godiya tai masa sallama ta yi dakin Yaa Buhari, Yau taci sa'a ta same shi yana shiryawa. Murmushi tayi tana murna zai rage mata hanya. ta ce, "Na Anty Zee barka da safiya!" Kallon ta yayi ya ce, "Barka kadai ya kika tashi?" Ta ce," "Lafiya Alhamdulillah! Yaya dan Allah...." Sai kuma tayi shiru Kallon ta yayi ya ce, "Dan Allah me?" Kai ta dan sosa tace, "Wallahi na makara gashi malamin mu ya ce Takwas muyi submitting din Assignment." "Ke kika sani!" Ya fada yana taje kan sa. Kallon sa tayi ta kalli agogon dake hannun ta. Ido ta zaro ta ce, "Inna illahi wainna illahir rajiun!" Ta fada tana fashewa da kuka. Kuka take sosai, tana bubbuga kafa a kasa kai kayi zaton dukan ta akayi. Kallon ta Buhari ya tsaya yi, dan inda sabo ya saba da halin Asma'u na shagwaba. Sai da yaga da gaske dai take sannan ya mike ya kamo ta. Kukan ta cigaba dayi shi dariya ma ta bashi. Da wannan kukan da ta tsaya yi ta dauki kusan minti uku dama zuwa tayi Baba ya kai ta amman ta tsaya. "Yi shiru yi shiru, shige muje!" Ya fada yana daukar hular sa ya saka Hannun ta ya kama sukai dakin Mami, gaisawa sukai ta tsaya kallon Asma'u ta ce, "Wannan kuma fa?" Ta fada tana nuna Asma'u. Dariyar Buhari ya danne ya ce, "Shagwaba daga ta makara sai kuka." Mami ta ce, "Ai Asma'u akwai wasa wallahi kasan Allah tin asuba bata komawa amman da ta gama taya ni aiki ta shiga wanka sai ta dauki kusan awa tana wanka bare shiryawa kuma tayaya baza ta makara ba." Murmushi Buhari yayi ya ce, "Uhm Ai "Asma'un Dady sai Dadyn. Mami mun tafi sai mun dawo." Ya kama hannun ta suka fice Asma'u na dagowa Mami hannu. Murmushi Mami tayi itama ta daga mata hannu. A ranta tana cewa, "Asma'u kenan." A mota ma haka ta dinga a zalzala shi amman ina tin a gida takwas da rabin ma tayi. Tana zuwa taga da malami a ajin a haka ta shiga ta zauna suka dinga amsar lecture. Sai da malamin ya fita Zainab ta karaso gefen ta tana dafa ta. Kallon ta Asma'u tayi fuskar ta dauke da damuwa. Ta ce, "Kiyi hakuri ki tashi muje ki kai masa ki bashi hakuri." Baki Asma'u ta rike ta ce, "zai amsa." Zainab ta ce, "Insha Allahu." Agogon hannun ta Asma'u ta kalla ta ce, "Sis kinga fa har sha daya." "Tashi muje insha Allahu zai amsa." Mikewa Asma'u tayi jiki a sanyaye suka nufi wajen office din malamai. Suna zuwa gefen office din Zainab ta ce, "Kije ki fito ina jiran ki." Fuska Asma'u ta bata zatai magana Zainab ta ce, "Kiyi hakuri kisan dai malamai basa son rakiyar nan ko?" Kai ta gyada ta tsaya ta kasa tafiya. Zainab ta ce, "Haba Asma'u kije man." Kamar bazata je ba kuma sai ta fara tafiya a hankali kamar wacce kwai ya fashe mata a ciki. Zainab na kallon ta tasan halin Asma'u zuwan ne bata sonyi. Take wannan tafiyar kamar me. Murmushi tayi ta karasa karkashin wata bishiya ta zauna. Asma'u kuwa ji take kamar ta juya gaban ta sai dukan uku uku yake a haka ta karasa har kofa office din da aka rubata *Sabir Marzuk* A hankali tayi knocking wanda ita kanta ba dan ita tayi ba da bazata ji ba. Sai da tayi irin knocking din nan sau uku sannan ta samu tayi da dan karfi. Izinin shiga ya bayar. Handle din kofar ta murda a hankali ta bude. Wani kamshin turare hade da sanyi me dadi taji yana tashi. A hankali ta kutsa kai ciki tana yin sallama kamar bata so. "Assalamu Alaikum!" Dago kai yayi jin muryar ta. Kallon ta ya tsaya yi kafin yai saurin kawar da fuskar sa, ya amsa da "Wa'alikum salam!" Kai tayi kasa dashi ta kasa magana. Shiru ne ya biyo baya na kusan minti biyu. Shi kam kallon ta yake kawai yana mamakin ta. Tsaki tayi a zuciyarta ta ce, "To me zan ce?" Da kyar ta iya dago kanta ta ce, "Uhm uhmm Sir dan Allah ina neman taimakon ka ne?" Kallon ta shima yayi ya ce, "Ok!" "Uhm Uhm!" Sai kuma tayi shiru. Murmshi yayi ya ce, "Ki saki jikin ki me zan taimaka miki dashi." Yai maganar cikin harshen turanci. Dan sanyi taji ji a ranta da bai mata rashin mutunci ba. Dagowa tayi suka hada idon. Idon ta Cike Da kwalla kamar zatai kuka. kallon ta yayi yai saurin kawar da fuskar sa. ta ce, "Sir Assignment nazo nai submitting" Kallon ta ya tsaya yayi, yana mamakin ta, 'wai Assingment tazo kawo wa." Asma'u ta ce, "Sir Kayi hakuri na zo a makare ne." Ta fada murya na rawa. Hannu ya mika mata kawai. Jakar ta tai saurin a jiyewa kan kujerar dake gaban table din sa. Dauko takardar tai a cikin wani littafi ta mika masa. Amsa yayi ya zubawa sunan ta ido. *Asma'u Suleiman* rubutun ya kalla yaga kamar computer ce ta rubuta shi. Sai da ya kai hannu ya shafa ssanan ya kara kallon sunan ya ce " *Asma'u Husnah* " Wata faduwar gaba Asma'u taji tai sauri dago idon ta. Dan duk duniya a wadan da ta sani take rayuwa dasu mutum biyu ke kiran ta da *Husnah* ko su ce, *Asma'u Husnah* sai kuwa yanzu da taji shi ya ambata. Sunan yai dadi da yadda ya kira ta sai taji kamar Yaa Aslan ne ya kira ta. Kai kadai ta gyada masa, ya ce, "Zaki iya tafiya." Jakar ta ta dauka, ta ce, "Nagode!" Ta juya a hankali ta bar office din. Zainab na hango ta ta mike ta ce, "Ya dai ya amsa." Kai kadai ta gyada mata ta ce, "Muje kar malama safiya ta shiga." Suka kama hannu suka tafi. Sai da aka tashi suka fito sukai sallah suka yi wajen Baba da yazo daukar ta. Munasha ce ta karaso gun da sauri tta ce, "Hae Babies!" Da sauri suka juya. Amsa'u ce ta danyi murmushi ta ce, "Sannu!" Zainab kuma ta hade rai tana yin gefe. "Baby an tashi ko ina Yayan ki?" Amsa'u ta ce, "Yana nan lafiya." Munasha ta ce, "Dan Allah wane irin aiki yake yi ne?" Asma'u ta ce, "Likita ne!" Ido Munasha ta bude ta ce, "Wow kace gidan ku kwari ne, amman ya dace likita. in kinje ki gaishen dashi." "Zai ji insha Allah!" Ta fada tana juyawa. Munasha ta ce, "Tnc bye!" Ta juya kawar ta na bin bayan ta. Zainab ce ta karaso ta ce, "Ke baza ki daina kula ta ba ko?" Fuska Asma'u ta marairaice ta ce "Ya zanyi kina ganin dai ita ke kula ni." Kallon ta Zainab tayyi ta ce, "Sai da safe." Ta shige motar gidan su. Kallon ta Asma'u tayi itama ta shige mota tana murmushi. *Yan uwa dan Allah ina barar addu'a ku in kunyi sallah ku sani a addu'a Allah biya min bukatuna na alheri* *Mutane da yawa na kira da min text na yadda suke jin dadin kasancewa dani nagode Allah ya bar kauna* Fatan alheri ga dukkan yan uwa musulmai tare da murnar shiga cikin sabuwar shekara. *Muna rokan Allah yasa mu dace. Allah kuma ya bamu ikon masa biyayya Allah ya sa muga wata shekarar da rai da Lafiya.* *Happy new Year* *INDABAWA* [1/18, 14:12] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* ASMA'U HUSNAH By *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* Dedicated to *My Ummi* *ALLAH BIYA MIKI BUKATUN KI NA ALHERI* *61-65* *Masu hikima sun ce: Rayuwa ta tambayi mutuwa, me ya sa mutane suke so na, amma ba su son ki? Sai mutuwa ta ce, saboda Ni Gaskiya cee Mai Daci. Ke kuma qarya ce mai cike da ado da Daukar hankali.* Tana zuwa gida ta shige tai wanka sannan ta dawo wajen mami dake falo. Mami ta ce, "Ya makaranta?" "Mami makaranta lafiya Alhamdulilah!" "Allah taimaka!" "Ameen! Mami Dady bai dawo ba, me kika dafa." Mami ta ce, "Shinkafa da miya." Mikewa Asma'u tayi ta dauki waya dan taji yanzu Dadyn ta zai dawo ko sai anjima. Yana dauka ya ce, " *Husnah* ya makarantar ne?" Murmushi tayi ta ce, "Dady har na dawo kuma Mami ta ce baka dawo ba yanzu zaka dawo ko sai aajima." Murmsuhi Dady yayi ya ce, "Sai anjima." Ta ce, "To Dady bari na kawo maka abinci kar ka ci na waje kaji." "To *Husnah* baki gaji ba." Kai ta girgiza ta ce, "Ban gaji ba Dady." "Shikenan kisa Baba ya kawo ki sai kin zo." "To!" Ta kashe wayar. Kitchen ta shiga ta hada musu abinci a katon basket sannan ta dauko jug ta zuba lemon da mami ta hada. Sai da ta gama hada komai sannan ta fito ta hau sama. wanka tayi ta saka atampa dinkin riga da siket ta dauki hijab iya gwiwa ta saka. Kasa ta sauko hannun ta rike da wayar ta. Tana sauka ta ce, "Mami sai na dawo!" Mami ta ce, "A dawo lafiya." Ta duko baske ta fita. Baba na gganin ta ya ttaso ya ce, "Sai ina kuma?" Ta ce, "Wajen Dady." Ya ce, "To muje!" Yai gaba tabi bayan sa. Suka dau hanya. Basu dade ba suka karasa office din Dady. Suna zuwa wani masinja yazo ya dauki basket din yayi offfice din Dady. Tana shiga ta dauki kudi a wata loka a cikin office din ta mika masa. Godiya ya dinga yi dai dai fitowar. dady daga toilet. Karasawa tayi tana cewa, "Dady sannu ya aiki?" Dady ya ce, " *Husnah* ke zanwa sannu kinje kinsha makaranta.." Murmushi tayi ta ce, "Dady yau ba gajiya kaga biyu mun gama komai." "To Alalh bada sa'a. "Ameen Dady!" Ta dauki basket din ta fara zuba masa abinci. Sai da yaci ya koshi sannan ta ce, "Dady bari naje wajen Yaya." "To a dawo lafiya." Ta fita. Knocking tayi a office din sa amman shiru. Tura kofar tayi kawai sai gannin shi tayi kwance ya lumshe ido yana amsa waya. Dagowa yayi ya zubo mata ido, ta ce, "Ina ta bugu yanzu da wani ne ya zo da sai dai ya koma." Hannu ya daura akan lips dinsa ya ce, "shitt!" "Naki nayi shiru." Ta fada tana dire masa fulas din a gaban sa tayi kan kujerar ssa ta office ta zuna. Juyi yake yi akan kujerar tana murmushi a ranta ta ce, "Wani lokacin tana nata office din tana duba mara sa lafiya." Dariya ta saki ta ce "Yaya dan Allah kallo ni a office dina." Baki ya tabe ya ce, "Ai ba kyau kikai ba." Dariya tayi ta ce, "Kyan kaga nayi.' Ta mike ta ce, "Uhmm bari naje na taya Dady aiki." Ta fice ta koma office din Dady. Gyara masa ta hau yi ta gyara masa ko ina ta share sannan ta zauna. Dady ya ce, " *Husnah* kenan sarkin aiki mijin ki ya huta komai kin iya ga tsabta." Murmushi kawai tayi ya zaro wayar sa ya ce, "Zo kiga kayan da aka turo sun miki naje na karbo ko wasu kike so." Ya fada yana dubo pics din. Matsowa tayi gefen sa ta zauna. Mika mata yayi ta dinga kallon kayan ta ce, "Masha Allah Dady sunyi." Dady ya ce, "Kin tabbata." Kai ta gyada masa. Ya ce, "Shikenan nan da sati biyu nake son tafiya. Da ba ckul da mun tafi tare." "Wallahi kuwa?" Haka suka zauna Dady na aiki tana taya shi hira har karfe shida tayi. Buhari ne ya shigo office din ya ce, "Dady ni zan tafi sai kun taho." Dady ya ce, "To muma fitowar zamuyi." Gefen Asma'u yayi ya mata rada. Hararar sa tayi ta mike. "Dady muje"" Ta yi gefen sa. Mikewa Dady yayi ta kamo hannun sa suka fito. A hanya kafin su sauka sai sallama akewa Dady jama'a sai gaishe shi suke. Dady mutum ne mai son jama'a da taimako kowa nasa ne. Dady yana da mutane sosai dan duk wanda ya kawo.kuka sa sai ya taimaka masa. Suna isa gida ana magariba dan haka parking kawai sukai suka yi alwala suka tafi masallaci. Asma'u kuma ta yi cikin gida sama ita ma tayi tai alwala tai sallah ta zauna har akai isha. Sanna ta sauko. Su Dady ta gani har sun shigo Mami na gefen sa. Mikewa sukai suka hau sama Dady ya watsa ruwa ya saka jallabiyya sannann ya sauko suka ci abinci Karfe Tara Asma'u tayiwa Dady sallama. sannan ta matsa gun Mami shima tai masa. Wajen Yaya Buhari tayi, tana murmushi kafin ta karasa ya mike. Kallon sa tayi ya ce "Lafiya?" Hararar ta yayi ya ce, "Abu zanje na siyo." Kallon sa tayi ta ce "Dan Allah Yaya ka tahon da ice cream dan Allah!" Wajen Dady yayi ya duka ya ce zai fita yanzu zai dawo sannan ya kalli Mami ya ce, "Mami me zan taho miki dashi?" Mami ta ce, "Ni ba komai a dawo lafiya." Ya juya zzai tafi Asma'u ta saki kuka. Da sauri ya juyo Dady ma ya mike da sauri. Mami kuwa da tasan halin ta yasa ta dauke kai. shi wanda yai mata laifin yafi kowa son jin me akai mata. Gun Dady tayi ta ce, "Dady ba Yaya Buhari bane, nace ya siyon aabu yai min banza." Kai Dady ya dago ya kalle shi. Shi kuma ya ce, "Haba kanwata ai naji wasa fa nake miki." Kai ta dago tana goge hawaye ta ce, "Da gaske?" Kai ya daga mata ta ce "To a dawo lafiya. Ni sai da safe." Ta fada tana mikewa tayi ta ce, "Dady Sai da Safe. Mami sai da safe." Suka ce, "Allah tashe mu lafiya" Ta nufi dakin ta. Yaya Buhari kuwa ajiyar zuciya ya sauke, ya fita. Mami ta ce, "Allah Dadyn Asma'u ku kuke sa Asma'u kara sa ta gainin yarinya ce. Yarinyar nan fa girma take ji abinda tayi sai kace yar shekara biyar." Murmushi Dady yayi ya ce, "To in ban kula da Asma'u ba da wa zan kula." Murmushi Mami tayi ta ce, "Ai shikenan tai ta zama aa yarinyar kuwa " Murmushi Dady yayi ya ce, "In girman yayi zata girma ne amman yanzu nawa Asma'un take. Dan dai tayi nisa a karatu ne kike ganin girman ta amman waasu kamar ta ma suna secondary school." "Ai kai dai baza ka taba yadda ba " Daga haka suka cigaba da hirar su. Asma'u kuwa tana shiga daki tayi wanka ta fito ta saka kayan baccin ta. Kan gado ta kwanta tana daukar wayar ta. Missed call din sa ta gani. Ido ta bude ta tafi kiran ta. Da sallama ya dauki wayar. Ido ta lumshe jin muryar sahibin ta. Kwanciyya ta gyara sannan ta amsa sallamar tata. "Baby na kina lafiya ya gida da makaranta?" "Lafiya lou Yaya na, ya su Momy da wajen aiki?" "Duk lafiya Alhamdulilah!" "Masha Allah!" " *Husnah* tin dazu nake kiran ki. zan zo wani aiki Kano nake son na fara fada miki." Da sauri ta mike ta ce, "Yaya dan Allah da gaske?" Kai ya gyada kamar yana ganin ta ya ce, "Da gaske zan zo nayi wata daya ne." Murmushi tayi ta ce, "Kai Alhamdulilah Allah kawo ka lafiya amman naji dadi wallahi. Yaushe zaka zo?" "Eh nan da sati biyu zan taho." Murmushi tayi ta ce, "Allah nuna mana." "Ameen!" Ya amsa. "Yauwah Yaya gobe zamu yi test ina son ka sani a addu'a." Murmushi yayi ya ce, "To Allah bada sa'a amman dai ni bana jin ki *Husnah* yanzu ma kafin ki kwanta ki dan duba littafin kinji." "Insha Allahu da asuba ma zan kara dubawa." "Yauwah Allah bada sa'a!" "Yanzu ki dauko littafin kiyi karatun awa daya zan kira ki anjima." "To!" Ta kashe wayar. Mikewa tayi ta dauko jakar ta. Test din Sir Sabir zasu yi gobe dan haka ta kuduri aniyar gobe da wuri zata fita. Sai da ta gama karatun kamar yadda Yaa Aslam ya ce, tayi sannan ya kira ta. Alwala yasa tayo ta shiga tayo tazo tai adduu'a ta kwanta. Karfe sha biyu Mami ta leko dakin taga Asma'u kwance akan gado. Addu'a tai mata ta tofa masa sannan ta fice. Don't forget to vote *INDABAWA* [1/18, 14:13] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR*  *ASMA'U HUSNAH* By *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* Dedicated to *My habibaty. My Ummu* *65-70* *Idan ka Dauki Alqur'ani Shedan yakan fusata. Da zaran ka bude shi sai ya fashe da kuka. Kana yin Bisimilla zai fadi qasa warwas. Da ka shiga cikin karatu sai ya suma ya fita hayyacinsa. Mu yi qoqari mu rinjayi Shedan* Washe gari kamar yadda ta tashi tin asuba ta tashi. Sallah tayi ta zauna tai karatun al kur'ani sannan ta janyo littafin ta ta kara dubawa ta jima tana duba littafin sannan ta mike ta sauka kasa. Mami ta dan kamawa abubuwa ssannan ta koma sama. Wanka tayi ta shirya cikin wata maroon kalar doguwar riga mai dogon hannu. Golding din takalmi da jaka ta dauka sai bakin hijab da ta saka iya kar sa kirji. Ba karamin kyau tayi ba fuskar ta tayi fes a ciki. Idonun ta sun kara gaske da girma girar nan tata a kwance luf luf. Leben ta sai kyallin man lebe yake. Dakin Dady ta shiga suka karya sannan tai musu sallama ta fito ta tafi dakin Ya Buhari. Yana zaune a gaban system ta same shi. Karasawa tayi ta ce, "To su Yaya me ake aka tashi da sasafen nan."" Bai kula ta ba. Dan durkusawa tayi ta gaishe shi. amsawa yayi yana dagowa ya kalle ta. Baki ya tabe ya ce "Baki kyau ba." Murmushi tayi ta ce, "Kyan kaga nayi." "Ahakan?" Kai ta gyada masa. "Uhmm dauki abonki afirij." Ya fada yana nuno mata firij din. Gun firij din tayi ta bude. Ice cteam ta gani a ciki dayawa. biyu ta dauka ta ce, "Yaya in na dawo na dauki sauran." Kallon ta yayi ya ce. "A dawo lafiya." Sannan ta fita. Dakin Mami taje tai mata sallama sannan ta sauka kasa. Baba yana ganin ta ya taso yayi wajen motar ya fito da ita. Sai da suka gaisa sannan ta bude gidan baya ta shiga. Kiran Yaa Aslam ne ya shigo dauka tayi, Bayan sun gaisa yake cewa "amman dai tana ckul ko?" "Aah Yaya yanzu dai zan tafk."" "Amman dai kinsan kin makara a yadda kika fadan kina da test ko?" "Ah haba dai!" "Eh man tara saura minti goma. Minti goma zai kai ki ckul ne." "Insha Allahu!" "To Allah bada sa'a sai kin dawo ki turon pics din ki ina jira." Ta katse wayar selfie ta dauka ta tura masa sai anan taga ashe dai da gaske Yaa Aslam yake ta makara ta tabbata nan da minti goma da kyar zasu karasa. Addu'a take Allah yasa kar ya shiga har sai ta shiga. A hankali Baba ya dinga jan su har suka karasa makaranta. Lokacin tara da minti goma. Da sauri ta fita daga motar. Hango shi tayi yana nufar ajin cikin takun kasaita yake tafiya. Yana sanye da golding kala shadda ya saka brow kalar takalmi da hannun sa rike da waya ya kara a kunne daga gani amsawa yake. Ba kara min kyau yayi ba. Fatar sa ta kara kyau da sheki. Gashin kansa ya kwata luf luf dashi. Ganin ya karasa ajin ma. yasa ta tsaya daga inda take hangen sa. Waje ta samu ta zauna daga gefen ajin ta kifa kanta akan jakar ta ta fashe da kuka. Ta dade tana kukan dan har karfe goma bata dago ba tana ta shesheka. Karfe goma dot ya fito daga ajin rike, da takardu a hannun sa. Yana karasowa inda take akai kiran wayar sa. Daukar wayar yayi, ya kara a kunnen sa yana kallon Asma'u da ta kifa kai. A wajen ya tsaya ya amasa waya, tana jin yadda yake maganar a hankali amman ta kasa dagowa. "Yanzu zan karasa office din kin karaso ne?" Ya tambaya. "Ok!" Kawai ya ce ya kashe wayar. Sai da ya kara kallon ta sannan ya bar wajen. yana barin wajen zainab ta karaso tana dago kanta. "Kuka!" zainab ta fada tana share mata hawaye. "Ba dole nai kuka ba. Wannan course din kar ya jawon Matsala fa" Ta fada tana kara fasa wani kukan. "Haka ne, amma kinsan Sir Sabir yana da sauki kai da kin shigo zai iya barin ki." "Haba Zainab sau nawa nake makara yake kyale ni so kike a fara kawo wani zargin bayan kinsan baya bari a shigar masa aji duk wanda ya makara daya ga ya shiga juyawa yake." "Kinga bar wannan zancen kije gun sa, kawai ki baahi hakuri kiji me zai ce, ya kara bada wani Assignment din ma in bai miki ba kinga kina da assignment balantana ma insha Allahu zai miki." "Uhmm fa Zainab kar naje yaki min. Ni dai wallahi na hakura" "Dallah can tashi muje!" ta kamo hannun ta suka nufi office din sa. A bakin office din ta bar ta. Yauma kamar rannan ta dade tsaye a kofar amman ta kasa kwankwasa kofar Cikin sanda ta dan kwankwasa. Izinin shiga ya bada. wata faduwar gaba ce ta sameta. A hankali ta daura hannun ta akan kofa, ta murda ta budo. Nan ma ta dau minti biyu kafin ta tura ta shiga. Tana shiga taji wani sanyi me ddi hade da kamshin turare na dukan ta. Tsayawa tayi a gun kafin tayi sallama. wata yarinya dake gefen sa, tana bude masa fulas din abincin data kawo ta zuba mata ido. Yarinyar zata yi shekara goma sha shida zuwa sha bakwai Kyakyawa ce suna kama da Sabir kamar kanwar sa. 'Yar yayar sa ce tazo musu hutu shine Mamah ta aiko ta, ta kawo masa abinci dan tasan halin sa da kyar zai ci wani abu gashi ya fito bai karya ba. Kallon Sabir yarinyar tayi ta daga masa kai. Ya ce, "Uhmm Maryam zo ki tafi nagode kar Mamah ta tafi ta barki." Maryam ta ce, "Kai Uncle wallahi Mamah ta ce, in tabbatar da kaci tukkunna " murmushi yayi wanda ya kara fitar da kyawun sa ya ce, "Da yake, ni yaro ne ko. Ko ni yaro ne, ina uncle din ki zaki ce sai naci abinci ne, maza zo ki tafi kice naci kinji." Ya fada yana daukar dankalin da aka soya a cikin kwai da attaruhu da albasa yana ci. Gefen kuma kunun gyada ne da yaji madara. Jakar ta ta dauka ta ce, "Allah Uncle haka zan ce baka ci ba." Tayi gefen Asma'u dake tsaye tana jin su. "Sannu!" Ta fada tana mika mata hannu. Dagowa Asma'u tayi ta kalli yarinyar kamar su daya da Sabir. Dan murmushi Asma'u tayi ta mika mata hannu ita ma suka gaisa. Murmushi Maryam tayi ta ce, "Sunana Maryam Suleiman ni 'yar yayar Uncle Sabir ce." Kallon ta Asma'u tayi da idon ta da suka canja kala ta dan yi murmushi ta ce, "Ni kuma Asma'u Suleiman!" Maryam ta ce, "Lah suna Baban mu daya amman wallahi Asma'u kin burge ni kawai naji ina sonki." Murmushi Asma'u tayi ta ce "Nagode sosai." Sabir dake zaune yana cin dankali yana kallon su ya ce, "To Maryam kije kar Mamah ta tafi ta barki dai Allah ke kadai zaki zauna a gida har magariba." Sakin hannun Asma'u tayi ta ce, "Na tafi sai nazo gun ki wata rana." Murmushi Asma'u tayi ta daga hannu tana mata bye bye har ta fita. Kai ta juyo ga sabir da ya zuba musu ido sai fitar da murmushi yake Tana juyowa ya mai da kan sa ga abinda ke gaban sa. Asma'u ta ce, "Sir dan Allah ka taimaka min!" "Dame fa?" Ya fada yana cin dankalin sa cikin kwanciyyar hankali. "Sir Test wallahi makara na yi shiyasa " Bai dago ya kalle ta ba ya ce, " *Husnah* wai ke kullun sai kin makara!" Da sauri ta dago kanta jin sunan da ya ambata. Ido suka hada wannan yasa tai saurin dauke kan ta. "Ji idon ki me ya same shi? Kuka ko?" Kai ta girgiza. "To mene?" "Ba komai." " *Husnah* baki ban amsa ba. Me yasa kike makara?" Shiru ta karayi. "Tin yaushe kike tashi?" Ya tambaye ta. Asma'u ta ce, "Asuba!" Kai ya jinjina ya ce, "Me kike yi har kike makara?" "Ba komai!" "Ba komai amman kuma kike makara?" Kai ta gyada. "Ki fadan abinda kike in kika tashi tin asuba." Kasa tayi da kai ta ce, "Mami nake dan tayawa aiki sai nai shirya. Kuma in nace bazan karya ba sai Dady ya zaunar dani sai naci. daga nan sai naje na tashi Yaya Buhari na gaishe shi na taho makaranta." Murmushi yayi jin yadda take maganar cikin shagwaba. ya ce, "Ku nawa ne a gidan ku?" "Daga Dady sai Mami, sai Yaya Buhari sai ni!" Ta fada tana wasa da hannun ta. "Kina da kanwa ko kani?" Kai ta girgiza ta ce "A'ah!" Ya ce, "No wonder ashe shiyasa kike shagwaba ko dan kece autah ko?" Fuska ta dan bata tayi shiru. Ya ce, "Eh mana. In ba haka ba menene na kuka dan baki shiga class ba." Shiru tayi ya ce, "Dauko takarda." Tai saurin ajiye jakar ta tana daukar wata takarda. Kujera ya nuna mata ya ce, "Zauna!" Ta zauna. question din ya karanto mata ta rubuta. Abincin sa ya cigaba da ci cikin kwanciyyar hankali. Sai da ya gama ya koma cikin office din inda aka zuba masa wasu hadadun kujeru da kayan kallo. TV ya kunna ya rage volume *Wai ya kuka gani? Shin wa yafi dacewa da Asma'u. Yaa Aslam ne ko Sir Sabir* *kuna jin dadin lbrin kuwa?" *INDABAWA* [1/18, 14:13] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *ASMA'U HUSNAH* By *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* Dedicated to *My soul mate. My Sweetheart Mamahh* *71-75* *Mai hankali yakan gane ko wane ne kai daga maganar da kake yi a kan mutane ba daga ma ganar da mutane suke yi a kan ka ba.* TV ya kunna ya rage volume yana kallo yana kallon ta sai rubutu take. Cikin minti latalin ta gama ta mika masa. Ta ce "Nagode!" "Uhmm please ungo amson maltina a cafeteria." Kin amsar kudin tayi tace zata siyo masa. Kai ya girgiza ya ce, "A'ah nagode karbi ki siyon ki siyo kema." Amsa tayi ta fice ta bar jakar ta agun. Tana fita zainab ta taso ta ce, "Ya akayi?" Murmuahi tayi ta ce, "Yayi min. Maltina zan siyo masa wai." Suka wuce cafteria suka siyo masa sanna suka dawo. Sabir kuwa Asma'u na fita ya bita da kallo sannan ya lumshe ido. A ransa ya na fadin. "Allah ka dauran abinda zan iya dashi." Yana mamakin duk rashin son maganar sa inda ya zauna yana tai mata wadan nan tambayoyin. Murmushi yayi tuno yadda take bashi amsar su. Yana nan zaune yaji knocking din ta. Izini shiga ya bata ta shigo. Tana shigowa ta mika masa maltinar sannan ta dauki jakar ta ta kara masa godiya ta juyo zata fita " *Husnah* " Ya kira sunan ta. Juyowa tayi, table ya nuna mata ta dawo tayi wajen. Kallon sa tayi ta ce, "Me zan miko maka?" Murmushi yayi ya ce, "Dauki wannan fulas din kije kici." Kai ta girgiza ta ce, "Nagode sir!" Hararar ta yayi ya ce, "Nace ki dauka ko?" Da sauri ta dauki fulas din ta ce, "Nagode!" Ta fice da sauri. Murmushi yayi ya dauki maltinar ya fara sha yana lumshe ido. Can ya mike ya dauki paper da tayi rubutu a jiki. Rubutun ta mai kyau ya bayyana karantawa ya fara yi yaga duk tayi dai dai. Lallai yarinyar tana da kokari da haka a assignment din ta ma tafi kowa marks. Tana fita ta mikawa Zainab fulas din hannun ta. Amsa tayi ta ce, "Wannan kuma fa?" "Wallahi Sir ne wai dole sai na amsa." Budewa zainab tayi kamshi ya doki hancin su. Anan suka tafi cafeteria suka siyo lemo suka wuce aji suka ci. Fulas din Asma'u ta wanke ta ce, "In zai tafi na mika masa." Anan take bata labarin Maryam yar gidan Antyn Sir Sabir. Zainab ta ce, "Kace yau kin hadu da yar uwa irin ki mai magana " "Dallah ni ina da surutu ne." Dariya Zainab tayi ta ce, "Ke zan tambaya. Allah yarinya jibi ki fito da wuri dan zai amshi assignment ba ruwana." "Insha Alah takwas ma na fito." "Alah yasa." "Ameen!" Suna zaune da yamma bayan sun gama lecture tana jiran fitowarsa taga shiru shiru gashi har anzo daukar Zainab wannan yasa ta nufi office din shi. Knocking tayi. Yana ciki a kwance ya kasa tashi ya tafi gida duk jikin sa ya mace. Jin knocking din ya gane nata ne dan haka ya mike kawai ya dauki jakar sa da basket din da Maryam ta kawo masa abinci. Kofar ya bude sukaci karo da juna baya tayi zata fada yai saurin riko ta ta dawo jikin sa. Da sauri ya dago ta yana fadin. "Sorry!" Baya ta ja a hankali ta ce, "Ba komai. Daman fulas din ka na kawo maka." basket din ya mika mata ya ce, "Muje na saka a mota." Ya rufo office din ta biyo bayan shi. A hankali yake tafiyar itama tana biye dashi har suka karasa wajen motar. Kujere me zaman banza ya bude ta ajiye masa fulas din tai masa godiya ta juya zata tafi, " *Husnah* " Ya kira sunan ta. Juyowa tayi, ya ce, "Kizo na rage miki hanya man." Kasa tayi da kanta ta ce, "Lah sir nagode nasan anzo dauka ta ma." "Oh sai anjima!" ya shiga mota Hannu ta dan daga masa ta juya ta nufi gun drivern su. Shiga tayi suka wuce a gida. Tin a mota suke waya da Yaa Aslam har ta karasa gida basu gama ba. Ganin Mami a falo yasa ta tsinke wayar ta fada kan ta tana cewa "Wash!!" Mami ta ce, "Ji zaki karya ni " Murya Ta shagwabe ta ce, "Mami na gaji." "Kije ki watsa ruwa ki dan kwanta ki huta kafin magariba." Mikewa tayi ta yi sama tana dailing number Ya Aslam. Wayar suka cigaba dayi tana karasawa daki ta fada kan gado ta ce, "Wash! Allah Yaa Aslam na gaji " "Ayyah sannu baby na ko nazo nai miki tausa ne." Murmushi tayi ta ce, "Da kuwa naji dadi." Murmushi yayi ya ce, "To kwanta ki rufe idon ki." Kwanciyya tayi ta lumshe idon ta. ya ce, "Yauwah bari a fara ta kafa ko?" "Wallahi kamar kasan sun gaji kuwa." A hankali ya dinga cewa na miki nan na miki amcan kai ka zaci da gaske tausar yake mata. Har akai magariba sannan sukai sallama ta mike ta shiga tai wanka ta fito ta tada sallan. Sai da tayi isha'i sannan ta mike ta nufi dakin Yaa buhari ta dauki ice cream sannan ta sauka kasa duk agajiye. Dady ta sama a zaune gefen sa Mami sai Yaa buhari a can gefe. sannu da zuwa tai musu ta zauna gefen Dady tana cewa "Dady wallahi yau na gaji da yawa." "Ayyah sannu Autar dady." "Yauwah!" Dady ta mikawa ice cream din ta ce, "Dady bismillah!" Murmushi yayi ya ce "Nagode!" Muje to kuci abinci. Ta fada tana mikewa. Binta sukai ta zuba musu ita kuma taja gefe tana shan ice cream. Yaa Buhari ya ce, "Dady kaga ko shiyasa da bazan siyo mata ba dan nasan ba son cin abinci take ba." Dady ne ya kalle ta ya ce, " *Husnah* ajiye kici abinci kinji." Ajiyewa tayi ta dan tsakuri abincin sannan ta ce ta koshi ta fara shan ice cream din ta. Suna gamawa tayi sama dan yau a gajiye take. Kwanciyya tayi ta jawo waya ta lalubo number sa. Lokacin shima yana kwance aka katon gadon sa sai juyi yake ta kira sa. Da sauri ya dauka ya ce, "Baby na lafiya?" "Uhmm lafiya lou! Yau na gaji shi yasa nazo na dan kwanta da wuri." Ya ce "Nifa ince nasan I yanzu kina gun Dady." "Yau na baro Dady da wuri." Ya ce, "To muyi hira." Shiru tayi ta ce, "Ka kawo hirar to." Ido ya lumshe ya ce, " *Husnah* ina bukatar muyi aure wallahi. Dan na fara kosawa zama ni kadai in dawo daga aiki bame min oyoyo bare ingan ki naji dadi." Murmushi Asma'u tayi. ya ce, "Dani dake na shirya, aure kawai nake bukatar muyi. Kuma nasan ko yanzu nace ayi za ai mana" Asma'u ta ce, "Yayana ai lokaci ne." "Uhmm haka ne, *Husnah* kin jefon kifiya tazo ta soken a zuciya ta. Amman sam ban ji zafi ba ko haushi, saboda kin turan abu me dadi a cikin ta." Ido ta zaro tana dariya "Nayi arangama dake a cikin rayuwa kin shige cikin jikina, munyi shakuwar da babu batun rabuwa, na kira ki mallaki na, haka nima na zamo nakine babu fargaba a cikin rai na. saboda nasan irin son da mukewa juna." Idon ta a lumshe ta fara magana tare da murmushi a kan fuskar ta, "Nice mahadin ka sahibina. Har abadan dakai nake son rayuwa. Ko da rana ko cikin damuna zan tsaya ka ban gujewa dukkan ruwa. Na sanar dakai dukkan sirrika na. Babu wanda zaiji tinda ka adana. Kazama shalele na guna kaine dan lele. Hanyar mu daya ce zata bulle da mun shiga za'a kulle, dadi rayuwa da masoyi shakuwa aure burin ran mu kuma insha Allahu nan ba da jimawa ba zan zama mallakin ka ta har abada." Mikewa yayi daga kwancen da yake ya ce, "Kalaman ki na kashe min jiki da haifar min da kasance tare dake." Amsa'u ta ce, "Haka nima nake ji. Kamar yadda kake koren damuwa. kai ke kawar min da kishiruwa. Bani son muyi rabuwa. Na fison kasancewa dakai har abada. Wallahi yaa Aslam da kai kadai nake son rayuwa, son ka kadai nake so na mutu dashi. Wallahi in bakai mutuwa zan yi ko ban mutu ba zan zamo ina raye kamar gawa ne. kai ne rayuwa ta Yaa Aslam " Ya ce, "In bake ya zanyi. In babu ke nazama tarihi, abar batu na duniya. Gangar jiki ce ke duniya amman ruhina da ke zasu kasan ce. Nafi son mutuwa ta raba mu" "Ban son maganar mutuwa ko rabuwar mu Yayanah." Ta fada muryar ta na canja wa. "Yi hakuri." Ya fada. Dan murmushi ta yi ta ce, "Ba komai. In munyi aure zan kula da Yaya nah!" Murmushi yayi ya ce, "Wallahi akan ki bana bidar shauki, nasan komai wanda zaki iya. Yadda dake nayi auren mu in anyi zamu more rayuwa. Nasan zaki kula dani ki ban duk hakkina." Ido ta rufe da tafin hannun ta. wai kunya. Tayi shiru. Ya ce, "Kina ji na?" Kai ta gyada tayi shiru Ya gane me yasa tayi shiru dan haka ya ce, "Wai kunyar nan fa tayi yawa. Ba damar nayi zancen aure. Bude naga idanun ki masu kyau da haske masu haskan zuciya ta." "Ya Aslam, Kai ne ka kasance abin anbato na a koda yaushe sai nayi tunanin ka. Dadi cikin kunnuwa na, zancen ka inkayi. ina son na kar kare rayuwa ta da kai. Ni gani nake sam babu wacce ta kaini dace, nice sarauniyar Mata." "Kin fi haka ma. in nace zan fadi yadda kike a cikin raina, watakila ki zata na haukace. son ki nasa naji ni a wata duniyar ta daban. Buri na kawai na gan mu tare a inuwa daya." "Allah nuna mana." "Ameen." Agogon dakin sa ya kalla ya ga har sha daya ta gota. Dariya yayi ya ce "Baby ina gajiyar ne?" Murmushi tayi ta ce "Yaya nah ya gusar min da ita." "Kinsan karfe nawa?" Kai ta girgiza. Ya ce, "Karfe shada da miti ashirin da uku." "Kai tab hira dakai tafi komai dadi a guna da dauken hankali na wallahi." Murmushi yayi ya ce, "To muje muyi alwala muzo mu kwanta." Ta mike shima ya mike suna dawowa sukai sallama kowa yayi addu'a ya kwanta. *INDABAWA* [1/18, 14:14] Maryam S Indabawa🥰:  *LABARIN RAYUWAR* *ASMA'U HUSNAH* By *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* Dedicated to *My Life. My momy* 76-80 *Manzon Allah(ﷺ)* Yana Cewa: *"Kuyi Aiki Domin Kowwa Ana Saukake shi ya Zuwa Abinda Aka Halicceshi Donshi ne"* (Bukhari da Muslim).* Ranar alhamis da wuri ta gama komai ta shirya tayi dakin Dady. Karfe takwas da arbain ta gama komai ta shiga dakin Yaya Buhari. Gaisawa sukai kawai ta fita duk dan kar ta makara. Shi kansa yau yasha mamakin ganin Asma'u bata tsaya jan magana ba. Baba ma da ya gama shiryawa ita kawai yake jira tana shiga ya tada mota suka nufi makaranta. Suna cikin tafiya motar ta tsaya. Fita Baba yayi Ya taba motar ya dawo amman shiru. Sai da yafita sau uku ana hudun Asma'u ta ce, "Baba me ya samu motar." Baba ya ce, "Asma'u kinsan ance karfen nasara bai da tabbas motar nan lafiya muku fito amman kinga ta tsaya taki tashi." Fitowa tayi ta duba agogo tara saura minti biyar. Waya Baba ya dauka ya kira mai gyara motocin gida ya fada masa inda yake Kallon sa Asma'u tayi ta ce, "Baba bari na hau napep dan na makara gashi zanyi submitting aasignment " "To bari na tsayar miki da Napep din.' "Aah Baba na gode." Ta fada tana dan matsawa. Mamaki take ganin karfe tara amman ji yan makaranta sai zirga zirga suke bama maza yan makarantun gwamnati. Duk Napep din da zai zo a cike yake zuwa. Wata Mota ce ta tsaya a gaban ta. Matsawa Asma'u tayi. Kara binta akai ta kuma matsawa. Fitowa yayi daga cikin motar. Wani hadaden saurayi ne ya fito. Fari ne, yana sanye da Ash kalar shadda kafar sa da bakin takalmi haka hannun sa daure da bakin agogo. Kansa bbabu hula sai gashi dake kwace luf luf. Yana da idanu, haka nan hancin sa dogone har baki. Karasawa yayi gun ta cikin nutsuwa ya ce, "Assalamu Alaikum." "Wa'aikulum salam!" Ta fada tana dan matsawa daga wajen. Kara bin ta yayi ya ce, "En mata ina zaki?" Ko kallon sa batai ba ta fara tsaida wani Napep. Bai tsaya ba sakomakon cikar da yake. "Naga kamar makaranta zaki kizo na rage miki hanya." Dagowa tayi ta watsa masa wani irin kallon sannan ta matsa wajen wani napep da ta tsayar. Kallon ta yayi har ta shige ciki sannan yayi murmushi ya shiga motar sa ya tafi. Tana zuwa ta tadda har an yi submitting ga wani malamin yana musu lacturrle. Kuka ta saka. tana zaune har lecturer ya fito. Ta shiga ajin ta kifa kanta a benci tana cigaba da kuka. Zainab ta matso gun ta tana bata hakuri sai ga. sir Sabir nan. A haka ya shigo har ya gama lecture Asma'u bata dago ba. Sai da zai fita ya dan matso gefen ta ya ce yana son ganin ta. Sannan ya tafi. Asma'u duk ta tsure dan tasan akan bai ga assignment din ta ba. "Zainab Allah bazani ba ni nagaji da kullum complain wallahi." "Kiyi hakuri kije baki san me zai faru ba." Da haka Zainab ta lallabata ta tafi office din nashi. Da sallama ta shiga bayan tai knocking an bata izinin shiga. Kai daga kallon ta ma zaka san ta sha kuka dan idon ta yayi ja dashi. Sir Sabir ne zaune a wata kujera sanye da Wata brown shadda. Gefen sa gayen da ta gani dazu a hanya ne yaso ya rage mata hanya. Waya taji Sir sabir yana yi yana cewa, "Ki nifa ban san ta ba a ranar nima na taba ganin ta." Shiru yayi sanna ya ce, "Sai kinzo. In kuma na fita ne shikenan." Ya kashe wayar. Kallon sa ya maida kanta ya ce, "Mene?" Kallon sa ta tsaya yi ta ce, "Uhmm uhmm!" Sai ku a tayi shiru. Fauwaz dake, gefen sa ya dago dan ganin da wa yake. Ido ya zaro ya ce "Kai kece?" Kallon sa tayi ta dauke kai ta ce, "Sir kace nazo." "Me yasa banga assignment dinki ba." Shiru tayi. Sai da ya kara nanata tambayar sannan ta dago ta kalle shi Fauwaz ne ya dago ya ce, "Friend ita ce wacce nake baka labarin na hadu da ita fa dazu. Motar suce ta lalace," Hararar sa Sabir yayi ya kalle ta ya ce, "Ke me yasa kullum kina da matsala ne, in tayi baki makara ba yau abu kaza ya faru me yasa ne *Husnah* " Fauwaz ya ce, "Haba aboki kayi hakuri man." Ya kalli Asma'u ya ce, "Beauty mene matsalar ki yanzu?" Banza tai masa tai kasa da kai idon ta na cikowa da kwalla dan ita da kai mata fada gara ka dake ta. Bata son fada a rayuwar ta yanzu zata fara kuka. Kallon ta Sabir yayi ya ce, "Mikon Assignment din naki kuma ki kara samun matsala na rashin submtting ko makara ki gani." Da sauri ta dauko ta mika masa. Ta ce, "Nagode!" Tayi hanyar fita da sauri Fauwaz ya mike zai bita Sabir yai saurin riko hannun sa. kafin ta bude kofa aka bude. Maryam ce ta shigo cikin shigar ta mai kyau ta saka doguwar rigar atamfa a mata dinkin mai dogon hannu. Mayafin ta dan yafa kai ba dan kwalli sai jaka dake kafadar ta. Tana ganin Asma'u ta saka dariya ta ce "lah Asma'u!" Sai kuma ta kama hannun ta. Ta kalli Sabir ta ce, "Uncle kace, baka santa ba a ranar ka taba ganin ta." Sai a lokacin Amsa'u ta tuno da statement din sa da ta shigo taji yana waya. Kamo hannun ta tayi suka shigo office din ta ce, "Ke nazo nema muyi sallama gobe zan koma garin mu gashi ban da number ki." Murmushi Amsa'u tayi wanda Fauwaz ya kasa dauke ido daga kallon ta. Hannun Maryam ta kama suka fita kallo Fauwaz da Sabir suka bisu da shi. Wajen Zainab suka karasa ta zauna sannan sukai musayar number sai hira ta balle. Dan har lecture tare suka shiga suka fito sukaje sallah sannan suka je cafteria suka ci abinci. Sai karfe biyar sannan suka rabu shima dan an tashi. Har bakin office din Sabir suka rakata suna daga mata hannu sannan suka juya. Sabir da ya zata ma ta tafi ta shiga ta zauna akan kujera ta ce, "Wash! Wallahi Uncle na gaji haka nima zan sha fama in na fara karatu." Kallon ta yayi ya ce "Daman baki tafi ba." Kai ta daga masa ta kalli Fauwaz ta ce, "Uncle Fauwaz ya kake?" "Ni ba ruwana da ke. Kin tafi kin barni." dariya tayi ta ce, "Ayi hakuri wallahi Uncle Fauwaz. Asma'u ce ta burge ni na dawo amsar number ta kasan gobe zamu shige." Kai ya daga ya ce, "Dan bani number na gani." "Tab ta ce, kar na bawa kowa wallahi." Sai lokacin Sabir ya ce, "In ba kwana zamuyi ba mu tashi mu tafi dare na yi biyar da rabi fa." Mikewa yayi ya dauki jakar sa da basket ya mikawa Maryam Amsa tayi suka fito tana ta basu labarin Amsa'u in ka kalli Sabir zaka zaci ba jin ta yake ba amman gaba daya hankalin sa na ga ita yana jin abubuwan da take fada. Da haka suka je gida haka tai ta bawa Mamah labarin Asma'u ranar dai har dare bata da magana sai Asma'u daga ta ce, tayi kaza sai ta ce tayi kaza. Ta ce, "Mamah baki ga ba yarinya karama ta na karanta medicine kuma a final year wallahi ta burge ni ga kokari da muka shiga lecture ita ke bada asma." Mamah ta ce, "Sai ki koyi da ita to." "Ai insha Allahu Mamah kuma nayi 'kawa." Shi dai yana zaune yana ji yana kara jin Asma'u na kara burge shi. Asma'u ma da taje gida sai da ta bawa Mami labarin yarinyar. Mami ta ce, "Daman haka rayuwa take wani na son ka wani kuma kin ka yake yanzu dai ita kince daga haduwa Allah ya sa mata son ki. To Allah ya bar mu ga masoyan mu." "Ameen!" Ta mike ta hau sama. Yaya Aslam ne ya kira ta bayan sun gaisa yake tambayar ta makaranta ita ma take tambayar sa wajen aiki. Soyayyar Asma'u da Aslam abin sha'awa ce da burge wa dan ba karamin son juna su suke ba kowa da son dan uwan sa son da basa son su taba rabuwa da junan su. Kowa na kula da tarairayar juna. Ga shi soyayyar su mai tsabta da kyau suke. *Haka rayuwa yake wani daya ganka yake jin son ka a zuciyar sa. Son Allah kenan wanda wani dabi'un ka su suka burge shi. Wani kuma halayar ka abubuwa da yawa dai. Allah ka bar mu da masoyan mu,* *Ameen!* Mutane na tambayata wai *Sabir* Mijina ne ko saurayi nane to daga *Sabir* har *Aslam* da *Fauwaz* all are my lovelly children. Really love then. *Husnah* kuma ina son sunan ne. *Masoya na nagode nagode Allah bar soyayya.* *Muje zuwa ga wani ya dadu a masoyan Asma'u shin ya kenan* *Ina mai bada hakuri na jina shiru da kukai jiya da night da na morning da ban ba. Nagode* *INDABAWA* [1/18, 14:15] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *ASMA'U HUSNAH* By *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* Dedicated to *My whole Number. My Momy!* *Allah kara girma da daukaka. Allah yasa ki gama da duniya lafiya. Ur love is special.* *81-85* *_An Tambayi *, *Manzon Allah(ﷺ)* Yana Cewa: *"Kuyi Aiki Domin Kowwa Ana Saukake shi ya Zuwa Abinda Aka Halicceshi Donshi ne"* (Bukhari da Muslim)._* Pretty ce zaune a gaban wani boka. Kai sufar bokan ma kanta abar kyama ce da tsoro bare kuma warin da yake yi. Abinda take bukata ta gama fada masa. buga kasa yayi yai dube duben sa sannan ya ce, "Kin kawo aiki me wahala dan mutanen nan ba a zaune suke ba wajen ibada sai dai zan san yadda zamu yi muga ta wacce hanya zamu bi." "Yauwah ni na fi so ma ita yarinyar a haukata ta yadda dole zai hakura da ita ko ta mutu ma." "Kull!" Yai mata wata tsawa ya ce, "Wannan yarinyar har tafi Aslam tsari da riko da addini baza mu iya da ita ba. Tafi karfin mu." Da haka ta zube masa kudi masu waya sannan sukai akan nan da wata daya ta dawo. Daga nan ma Pretty ba gida tayi ba wajen wani bokan ta karayi suka karai mata alkawarin komai zai wakana yadda take so. Da haka ta koma gida da murna abinda take so zai zo gare ta. Dan har ta fara shirye shiryen auren ta da Aslam. Aslam kuwa bai son wainar dake soyawa ba. Shi dai bai da buri da muradin da ya wuce ya ganshi tare da Asma'u. Kowa da yasan Aslam yasan Asma'u dan kowa yasan irin son da yake mata. Abokan sa har tsiya suke masa su ce, ya makalewa karamar yarinya me ya gani agun ta. Shi dai sai dai yai dariya dan son Asma'u daga Allah ne. Allah shi ya sa masa son ta a zuciyar sa yake jin bazai taba iya rayuwa ba ita ba. Yasha fadawa Asma'u bazai taba barin ta ba ko ya ce, "Ba zai taba daina son ta ko mata kishiya ba." Duk kishin Asma'u sai dai ta ce, "A'ah Yaa Aslam ka daina min irin wannan al kawarin Baka san me Allah ya tsara mana ba." Shi in ta fadi haka wani lokacin har haushi yake ji. Ita kuma tana tsoron ta sawa zuciyar ta haka Allah ya riga da ya tsara wani abun daban. Tana son Aslam tana kishin sa kamar yadda shima yake son ta da kishin ta. Dan yawancin wasu dogayen hijaban ta shi ya siyo mata dan zuwa makaranta. Daga doguwar riga sai hijabai su take sawa. ********* Munasha ce zaune da kawar ta. Kallon ta kawar tayi ta ce, "Wallahi ko mayya sai haka." Munasha Ta ce, "Da me fa?" "Wannan yaron mana Aslam dan Allah ki kyale shi ki kama samarin harkar yanzu ba kudi basa shigo mana sosai saboda kin rage kula su wallahi." Ido Munasha ta lumshe ta ce, "A duniya mutum daya na taba so kuma shi insha Allahu sai na aure shi shine Nazir. Ko da na rasa shi Kuwa na rasa shi to bazan rasa Aslam ba wallahi Aslam ya min surar sa abar so ce ga kowacce mace da tasan 'da namiji. Kingan shi kuwa," Ta girgiza kai ta kwanta wallahi ba wanda yanzu nake sha'awa in ba shi ba. Shi kadai nake son nai tarayya da shi sai kuma my oga at top." "Ni dai naji ki dauri kije gun Alhaji Usman kinsan babar harka ne, ko nawa kika nema zai baki kinga ko dasu masan yadda za ayi a jawo hankalin Aslam gareki." Munasha ta ce, "Kuma fa kin kawo magana wallahi dan Aslam zan je." Ta mike ta fada wanka cikin minti biyar ta shirya cikin wani dan mini siket wanda ana gano kasan ta. Sai yar half ves da ta saka ta bazo da gashin dakin ta gadon baya. Tayi kwalliyar karuwai ta jefa cingum baki tana tauna sai kara take dashi. Turare ta bade jikin ta dashi ta fita ta shiga mota sai guesthouse din Alhaji Usman. Yasan da zuwan ta dan yafi sati yana jiran zuwan ta. Yana falo a kwance yana trying number ta sai gata kamar daga sama. Kan cinyar sa ta dane, tana masa wani kallo tana shafa shi. Nan da nan ta burkita masa tunani tun a falo suka fara masha'ar su har suka koma daki. A ranar a gidan ta kwana dan washe gari ma kin barin ta yayi ta tafi. A kalla sai da tai sati biyu a gidan sannan ta tafi da milliyoyin kudi banda mota da ya mallaka mata. Haka ta koma gidan ta da ta siya ta tadda Bulkis. Mukkullin motarta ta da ta jefawa mata ta ce, "Na bar miki." Tsalle Bilki ta duka tana cewa da "Da gaske!" "Eh man! Kinsan ni yanzu na zama babar hajiya. Zan miki transper kudi. Amman ina son naje gida yau naga ya Baba take ciki." Bilki ta ce, "Sai yaushe kuma?" "Sati daya zan yi." Munasha ta bata amsa ta mike tana debo kayan da gida suka san ta dasu ta zuba a jaka ta shiga tai wanka ta saka wata kodadiyar atamfa dikin riga da zani. Tana fitowa Bilki ta saka dariya ta ce, "Amman fa da ace a haka kike da kin bada mata." Dariya itama tayi ta ce, "Ke dai bari baki ji yadda zanin nan ya dame ni ba." "Wai dan Allah satin.kuwa zakiyi dan Allah kiyi kwana biyu ki dawo." Bilkis tafada Munasha ta ce, "Aah bilki duk rashin iyaye na ina son su. Naje gun wani kato na yi sati biyu bare gun iyaye dan nayi sati. Aah wallahi." Baki Bilkis ta tabe ta ce, "Shikenan. Ki gaida su Baban." "Zasu ji " Ta dauki jakar ta tafi. Napep ta tsayar ya kai ta har gida. Kannen ta sai murna suke sun san zasu samu dan abin tabawa. Gun Babar ta taje ta gaishe ta. Baba sai addu'a take mata na samun nasarar karatu sannan ta gaida mahaifin ta. Kayan abinci ta siyo musu bubun shikafa da katon din tafiya da macaroni. Ta bawa Baba dubu goma Mama dubu biyar. Daman ta fada musu tana dan siyar da abubuwa a makaranta wannan yasa suke zaton tana take samun kudi. Duk abinda take akwai ta da ibada da biyayya ga iyayen ta. Dan ita tazo gida ita ke yin komai haka zasu ta sa mata albarka. Taje gidan su Nasir saurayin ta wajen kawar ta Rashida. Anan Rashida take labarta mata Yaya ya kammala karatu sun rike shi zaiyi aiki shekara daya ya dawo. Ba karamin murna Maimuna ta taya shi ba. Anan suke hira da Rashida akan makaranta. Rashida ta ce, "Maimuna ki godewa Allah duk cikin mu ke ce kika samu jami'a mu duk sai kwaleji. Dan Allah ki dage ki fito da sakamako mai kyau. Kinga karatun nan shine gatan mu da na iyayen mu da ya'ya mu. In muka samu aiki zamu tai makawa iyayen mu. Ya'yan mu kuma mu koya musu. Dan Allah ki dage kinga sauran shekara daya da rabi kigama kinji." Sosai Maimuna taji fadan Rashida kuma tasa a ranta zata tsaya tayi karatun ta gama lafiya. Satin ta daya ta fara shirin komawa ita kan ta ji take kamar kar ta tafi amman kuma tana so taje ta tana din rayuwar ta tanan gaba. Sannan tasa a ranta wannan karan zata tsaya ta fuskanci rayuwa tai karatu dan tasan tabbas karatun nan shine gatan ta. Karuwan ci na dan lokaci ne in kuwa kana da ilimi ka samu aiki kana samun kobo da naira. Da kuka ta tafi kannen ta suma sai kuka suke. Tinda Munasha ta koma makaranta take karatu sosai. Duk wanda tasan yana da kokari tai ta bibiyar sa kenan su kuma suna wulakanta ta suna zaton ba da gaske take ba. Sai da suka ga da gaske take sannan suke koya mata. Harka da maza kuwa tanayi jifa jifa amman yanzu kudi take tarawa bata fiya shaye shaye da siyi banza siyi wofi ba. Kawayen ta da dama sun ja baya da ita dan ta rage kashe kudi da siyan kayan maye. Bilkisu ce kawai suke tare itama kullum sai ta ziga ta amman bata dauka. Wani lokacin sai taji kamar ta dauka sai kuma ta fasa. Yau ta kama Asabar tinda Asma'u taje makaranta ta dawo ta shige daki take bacci Yaa Aslam ya kira fin sau goma amman bata ji ba dan a silent wayar take. Ba ita ta tashi ba sai hudu saura tin sha biyu da rabi take abu daya. Wanka ta shiga tayi tayo alwala duk da bata sallah tana yin alwala dan alwala tana da tasiri a jikin dan adam. Mai ta shafa ta hau kwalliya sai kace wacce zata biki. Sosai ta fente fuskar ta da yake Asma'u akwai son kwalliya wannan yasa taje ta koya to makaranta ke hanata zama tayi. Wani Golding codeless ta dauko ta saka. Dinkin doguwar riga daga sama ta kamata daga kasa ta bude. Mayafi ta dauko maroon kala, karami ta yafa jikin ta ta hade turaruka sannan ta dauki wani maroon kalar sandal ta saka. Turare ta kuma yin wanka dashi sannan tafi daga dakin ta. Tafiya take a hankali har ta karasa dakin Yaa Buhari. Firij ta bude ta dauki robar ice cream din ta, ta sauka kasa. Tafiya take a hankali tana sauka idon ta na kan wayar ta da taga missed din Yaa Aslma. Har ta karasa ta zauna sannan ta dago kanta. Wa zata gani!!!??? *Ina mika sakon gaisuwa ga duk masoya na. Allah ubangiji ya kara kauna da zuminci. Dukkan ku ina yin ku.* *Nagode* *INDABAWA* [1/18, 14:15] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* *Gidan Amanci da albarka* Dedicated to *My Lovelly Momy* Allah ya gafarta miki duk kura kuren ki. Allah ya dada tsawan kwana ya sa Aljanna makoma. *Ameen!* 86-90 *_*Manzon Allah(ﷺ)* Yana Cewa: *"Lallai Abin Sani Maji6incinsa Shine: Allah da Kuma Muminai Na Kwarai"* (Bukhari da Muslim)._* Dagowa tayi wa zata gani. Ido ta kara budewa tana kare masa kallo. Sanye yake cikin Shadda Cream kala, kansa ba hula gashin nan ya kwanta luf luf. Idon sa sun kara girma da haske sai hancin sa da ya kara fito wa. Dan karamin bakin sa ya kara zama pink sai sajen dake gefen fuskar sa da ya kara fito da kyan sa. Murmushi yake mata hakoran sa farare suka bayyana hadi da lobawar kumatun sa. Mikewa tayi tana kallonsa sannan ta karasa gun sa. Hannun sa ta kama. Sai kuma ta saki murmushi ta ce, "Wai mafarki nake ne?" Hannun ta ya kamo yayi saitin bakin sa ya zura sannan ya dan ciza. Da sauri ta kwace hannun tana yarfewa ta ce, "Yaa Aslam da zafi fa." Murmushi yayi ya kamo hannun yana hura mata iskar bakin sa. Ido ta lumshe ya ce, "To ai naga baki yadda ni din bane." Murmushi tayi ta bude ido. Ya ce, "Missed nawa kika gani tinda zan taho nake neman number ki amman ba a dauka ba." "Wallahi sai yanzu na gani. Bacci nayi." Ta bashi amsa tana zuba masa ido. Shima idon ya zuba mata, sun dau mintina. a Haka kowa ya kasa daina kallon dan uwan sa. Kamar yadda Asma'u tayi kyau a idon sa ita ma haka taga kyan sa. Hannu ya dago yayi wajen idon ta dashi yace, "Wannan da wannan da wannan suna burge ni." Ya nuna idon ta da hancin ta da dan karamin bakin ta. Dariya tayi ta ce, "Su kadai ko shikenan tinda su kake so ka cire na bar maka." Murmushi yayi ya ce, "To ai kinga wanda na fiso gaba dayan ta nan." Ya nuna ta. Dariya tayi ta yi kasa da kanta. " *Husnah* kinyi kyau. Wallahi kin fi kyau a fili akan hoto. Hoto yana ragen kyan ki. Kinga yadda kika kara girma kuwa. Allah ko yanzu ai mana aure nasan zamu samu babies ko?" Ya karasa fada yana mata rada a kunne. Mikewa tayi zata bar gun ya kamo hannun ta. Komawa tayi ta zauna ta yi kasa da kanta. Murmushi yayi ya ce "Ko ba zata iya samu bane." Duka ta dan kai masa, ta ce, "Kai Yaa Aslam ko gaisawa ba miyi ba." Ta fada dan ta kautar da maganar. Dariya yayi ya ce, "Wayo ko? To ina yini Baby nah, ya kika tashi daga bacci kin yi mafarki na. Na miki kiss ko? Na miki....." "Haka ake gaisuwar" tai saurin katse shi. Kai ya dan sosa, ya ce, "Ya ake yi. Kinsan in ina tare dake komai yakan bace min." Murmushi tayi tace, "Wannan Yayan nawa." Shima ya ce, "Wannan Kanwar tawa." Sukai dariya gaba dayan su. Sannan ta ce, "Yaya ya hanya?" "Lafiya Alhamduliah! Sai kika ganni ko?" Kai ta gyada ya ce, "An rage mana sati daya ne, shine na taho." "Amman naji Dadi, ina Momy da Dady " ta tambaya. Ya ce, "Suna nan lafiya suna gaishe ki Dady ya bada sako a baki." Murmushi tayi ta ce, "To nagode!" Dakin ta kalla ta ce, "Yaushe kazo ne?" Ya ce, "Tin karfe biyu." "Kaci abinci.?" Ta tambaye shi. "Kema kinsan Mami baza ta bar 'dan ta da yunwa ba." "Uhmm ina Mamin take ne?" "Tana dakin ta. Dauko mana ice cream din musha kar ya narke." Mikewa tayi ta kawo suka fara sha yana bata a baki har suka shanye. Hira suke abinsu kamar me, in ka kalle su sai sun baka sha'awa dan sun dace da juna. Sosai take bashi labarin ckul din ta shima yana bata labarin yanayin wajen aikin su. Har akai magariba ya tafi yayi sallah ita ma tayi sama. sannan suka dawo falo. Mikewa yayi zai fita ta ce, "Ina zaka?" "Ina zamu dai?" Ya fada yana nuna mata waje. Mikewa tayi tabi bayan sa. Garden din gidan suka nufa suka zauna a kujera suna facing junan su. Indai Yaa Aslam yazo kano nan ne wajen zaman su, " *Husnah* ina son ki ina kaunar ki kece farin ciki na kece rayuwa ta." Murmushi tayi. tayi kasa da kan ta Kallon ta yayi ya ce, "Duk adadin zancen da zan miki *Husunah* bazan yi san rai na ba. sako na zuciyata bakina ya furta ido ba bazai boye ba. kinyi kyau ke mai kyau ce, abu da zan sa ai mana. Zan sa ai mana sahamaki, abadan bazamu rabu ba." "Sha makin me?" Asma'u ta tambaya. "Aure man! Asma'u aure shine shamakin da bazai taba raba mu ba." Murmushi tayi ta ce, "Ka iya Sassauta harshe ka wajen fada min abinda zai min dadi. Ya Aslam Wani lokacin ina tsoran kar ka guje min dan duniyar ga da fadi. Dare da rana ban da burin da ya wuce muyi tadi." Murmushi yayi ya ce, "Asma'u kenan Kimin hukunci yadda ya dace a sanda nai.miki laifi. Amman sai ki min adalci a sanda bani da laifi. In kuma naki na baki kulawa ki hada rami me xurfi. a sanda na canja wani hali kimin nasiha baki guje ni ba. Ki fahimce ni aduk abinda zan miki ki auna kiga a wane hali zan miki abin. Ni dai nasan a cikin hayacina bazan taba miki abinda bakya so ba." Asma'u ta ce, "Yaya Aslam kamar yadda Kayi dakon soyayya ta a ko ina ka bayyana ta a fili ina gudun masu yin kwace su san ina da dalilin son da nake maka kar su kwacen ka. Tarrayar mu dakai bata da karshe dan zuciya ta da son ka ta girma ta rayu kuma da son ka zata mutu." Murmushi yayi ya ce, "Asma'u kenan ba wacce zata kwace miki ni. Ni naki ne ke tawa ce." Shiru tayi sannan ta dago idon ta har ya sauya kala. A kidime ya sauko daga kujerar da yake, yana tambayar ta "Menene? Me nayi miki?" Kuka ta fashe dashi. Jikin sa ya janyo ta yana lalashin ta har ta samu tayi shiru sai ajiyar zuciya da take sauke da karfi Bayan ta yake shafawa a hankali har ta koma sauke ta a hhankali. Dago ta yayi ya ce, "Me nayi miki?" Kai ta girgiza. Ya kalle ta ya ce, "Dan Allah ki fadan me yake damun ki zan fiki shiga damuwa in baki fada min ba." Kuka ta kuma fashe da shi ta ce, "Wallahi Yaa Aslam ina jin tsoro! Ina jin tsoron kar na rasa ka." Sai ga wani kukan nan. Rumgume ta yayi tsam yana jin wani son ta na kara ratsa shi. A hankali ya fara magana. Ya ce, "Asma'u kinsan wani abu kuwa. Nasha yin istihara akan al amarin mu amman a ko da yaushe kara jin son ki da kaunar ki nake. Wannan ya nuna min cewa *ke alheri ce* dan in da ke ba alheri bace da Allah zai na yayen son ki na. Asma'u tin kina yarinya nake son ki tin baki da abinda za'a so ki dan haka ki daina sawa wani abu zai sa na rabu dake, ki daina tsoron komai ki dauka ni naki ne, ke kadai. Kamar yadda kema zaki zama tawa ni kadai. Haba ni dai nasan *Husnah* *tawa ce* " Ya dago da kanta yana goge mata hawaye. Mikewa suka yi. Ya ce, "Smile!" ai kuwa sai ga shi nan ta saki murmushi, ya kai hannu zai taba dimple din ta tai saurin kaucewa. Zama yayi yana dariya, ya daga hannu ya kira ta. Alamar tazo. Kai ta make, murmushi yayi ya ce, "Zo mu zauna dake masoyiya na amince dake a zuciya, aure na dake na shirya amana zan rike ba gajiya. Tinda kin min so na gaskiya, dan haka ban barin ki kisha wuya. Zan kula dake zinariya." Matsawa tayi gunsa, ta ce, "Naji dadi wazai min murna, nayi godiya a gareka, tinda kakira ni matar ka, zana baka dukan hakkin ka, ni bazan yadda a kushe ka ba. Tinda na yaba da halin ka saboda iya takun ka natsuwar ka, da tsarin ka ni na so ka. Na zo mu zauna dakai a rayuwa na amince dake muyi auren sunnah." Kallon ta yake yana mamakin kalaman ta, dan yasan ba sosai Asma'u ta fiya magana a gaban sa ba saboda kunyar ta. ya ce, "Ni dake zan daura aure na zamo ango ke amarya, dakina a gidana zaki tare ki rangada kwalliya ki min ado me kyau. Farin cikin zaya daure, hawayen ki ni zani share, dake zan zauna na more. Miyi rayuwa mai inganci bazan taba saki kuka ba." Ta ce, "Kai ne zabi Allah yayi mini. Naji dadi kuma kayi mini. Ga hannu na kama ka hayar mini. Gidan aure ka kaini ka ajiye ni. A mata zai zama babu kamar ni. Matsayi mai girma zana baka. In kula dakai muyi soyayya mai tsafta da rikon amana." Mikewa yayi ya matso gun ta. Kasa tayi da kanta. "Oh my God! Ji yarinya sai kace bake kika gama magana ba yanzu kuma sai kunya. Wannan kunyar taki." Ya fada yana nuna ta sai kuma yayi kwafa ya ce, "Zan cire tane, wata rana sai kin manta da kin taba jin kunya ta kamar haka." Mikewa yayi ya kalli agogon hannun sa. Ya ce, "Tashi mu shiga ciki tara saura." Da sauri ta dago ta ce, "Dan Allah da gaske?" "Zo ki gani." Tayi wajen sa. Rumgume ta yayi ya nuna mata. "Uhmm to sake ni, Dady ya dawo tin dazu." "Muna nan soyayya bamuji shigowar sa ba." "Kai kayi soyayya ni banyi ba." Ta fada tana yin gaba. Kamo ta yayi ya ce, "Au ke bakiyi ba?" Kai ta girgiza masa ta ce, "Ni kuwa nayi soyayya." Sakin ta yayi ta dan matsa ta juyo ta ce, "Ina ni ina soyayya da yaya nah. Wallahi kunya nake ji." Ta ruga a kuje. Murmushi yayi yabi bayan ta. Falo ta shiga tana haki kallon ta Dady yayi ya ce, "To fah Aslam yazo an manta da Dady ko *Husnah* " Gun sa tayi ta ce, "Aah wallahi ban san dare yayi ba muna garden!" *Husnah-Aslam* *Husnah-Sabir* Na sameku lafiya ya al amura. Allah ubangiji ya taimake mu. Ameen Nagode masoya masu comment da masu like da kowa ma. *INDABAWA* [1/18, 14:16] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers Association * *Gidan Amanci da albarka* Dedicated to *My Lovelly Momy* *Mahaifiya ta abar alafahari na. Allah ya sa ki gama da duniya lafiya*zn 91-95 *Wani mutum yacewa Hasanul Basry:Ya Aba Sa'id ina kawo maka kukana akan 'Ke'kashewar zuciyata saiyace masa:Ka ladabtar da zuciyarka da ambaton Allah* Aslam ne ya shigo shima gefen Dady yayi shida Asma'u suka sa shi a tsakiya suna masa sannu da zuwa. Yaya Buhari ya ce, "Wallahi Mami a gidan nan ba a so na." Sai a lokacin Aslam ya kula da shi. Dariya yayi ya ce, "Aah 'kanina ashe ka dawo," Kai ya dauke wai yayi zuciya. Dariya sukayi. Asma'u tayi gefen sa ta ce, "Sannu bro ya aiki?" Banza yai mata. Kukan karya ta fashe dashi in kaji yadda ta fashe dashi kayi zaton na gaske ne. Nan da nan Yaya Buhari ya jata yana bata hakuri. Dariya ta saki ta ce, "Daman nace sai ka.kula ni." "Kai amman yarinyar nan kinga lago na." Ya fada yana daga ta daga jikin sa. Daga haka suka hau hira. Har karfe goma suna falo sannan Aslam da Asma'u suka tafi gun cin abinci. A can ma sun jima suna hira sannan suka ci abincin cikin so da kauna. Aslam ya ce, " *Husnah* ji nake ina ma anyi abin nan gidan mune mu sha soyayyar mu." "Lokaci dai. Allah nuna mana." "Ameen! Allah har na hango yadda zamuyi soyayya nake." "Kai Yaa Aslam! Kana son soyayya." "Dole naso ta *Husnah* dan wanda bai soyayya bai son dadin duniya nan ba soyayya tayi. Allah kuma ya bar mu da masoyan mu." "Ameen!" sannan suka mike suka koma daki. Sallama sukai wa su Dady kowa yayi dakin baccin sa. Duk abinda ta saba tayi sai da ta gama su sannan ta kwanta. A haka ma sai da suka kara yin waya kafin su kwanta. Sun jima suna waya sannan sukai sallama bayan sunyi alwala. Washe gari lahadi yini sukai tare. Ko gajiya da zama tare ko hira basa yi. Sai dai ka jiyo murmushin su ko kaji dariyar su. Mami dai bar musu falon tayi, haka suka yini a gidan. Tare suka ci abinci suka yini sallah ce ke daga su. Bayan sunyi sallahar la'asar, ne ya ce, Asma'u ta shirya ssu fita. Wanka ta shiga tayi, ta fito ta saka Wata doguwar riga fara an mata ado da jan stones sai Jan mayafi da jan cover shoe. Wata jar jaka ta dauka. Turare ta fesa ta fito tai dakin Mami. Mami na zaune tana kallo Asma'u ta shiga Kallon ta Mami tayi ta ce, "Sai ina kuma?" Murmushi Asma'u tayi ta ce, "Zan raka Yaa Aslam ne." "Toh! A dawo lafiya." "Allah yasa." Ta mike tayi waje. A kasa ta samu Ya Aslam ya na sanye da farin wando da jar riga. Takalmin kafa sa ma ja ne. Sai tashin kamshi yake yayi kyau. Yana ganin Asma'u yasaki murmushi ya ce, "Wow My baby tayi kyau munyi anko." Murmushi ta yi ta ce, "Ka fini yi." Wayar sa ya zaro ya ce, "Zo mu dau selfie." Gefen sa ta karasa ta tsaya matsowa yayi jikin ta, ya dauke su. Ya musu fin kala biyar sannan ya dinga daukar ta. "Yaa Aslam ya isa haka." Ta fada saboda taga ba alamar tsayawa. "To muje." Ya fada yana kamo hannun ta. Fita sukai ya karasa gun Baba ya amso key mota suka shiga. Shoprite suka shiga suka wuce cinema. kallo suka danyi sannan suka fito suka shiga ciki. Sun shiga suka nufi gun kayan sakawa. Sosai yake jidar mata dogayen riguna masu kyau da tsada. Haka ya nufi gun takalma da jakun kuna. Sosai ya kashe mata kudi sannan suka nufi gun alawa ya siya mata ice cream. Bayan anyi total ne aka dibi kayan akayi wajen mota dashi. Suna tafe suna hira taji ta bugi abu tayi baya zata fadi. Da sauri ya rikota ta fada jikinsa. Kafin ta dago taji Yaa Aslam ya dago ta yana cewa, "Ba dai matsala ko?" Kai ta daga masa, kamshin turaren da taa shaka shi yasa tai saurin dagowa. Ai kuwan shine, yana sanye da bakin wando da jar riga, yayi kyau sosai dashi. Ba kowa bane face Sir sabir. "Sorry!" ta furta a kasan leben ta. Yaa Aslam ne ya kama hannun ta suka bar wajen. Sabir kowa kallo yabi su dashi. Yana me lumshe idon sa. Suna fita ya ce, "Sannu Baby na ko na dauke ki ne." Kai ta girgiza ta ce, "A'ah nagode zan iya tafiya ai." A hankali suka karasa gefen Mota suka shiga suka bar wajen Suna zuwa gida ana kiran sallah isha'i Daki suka shige sukai sallah sannan suka sauko kasa. A kasa suka samu har Dady ya dawo. Saannu da zuwa sukai masa sannu da zuwa Abinci suka ci sannan suka koma falo ana hira. Sai karfe tara suka tafi makwancin su. Washe gari Monday. Tana gama abinda zatai ta shirya cikin wata pink kalar doguwar riga. Milk mayafi da takalmi ta saka. Sai pink kalar jaka. Batai kwalliya ba fuskar ta daga hoda sai man lebe. Wajen Dady taje. Tare suka karya. Sannan ta fito. Yaa Aslam ta gani a falon sama. Karasa wa tayi gun sa. Yana sanye da Bakin wando sai blue kalar riga mai dogon hannu. Yayi kyau sai tashin kamshi yake. "Yaya nah ina kwana?" Ta gaishe da shi tana zama a hannun kujerar da yake. "Lafiya lou. Ya Baby na ta tashi." Murmushi tayi ta ce, "Lafiya Alhamdulilah." Sannan ta mike ta sauka kasa. Basket din abincin sa ta dauko wanda ta zuba masa komai a fulas din sa. "Mu tafi?" Ya fada yana tambaya. Kai ta gyada masa, dakin Mami suka yi sukai mata sallama sannan suka wuce zasu sauka. Mantawa tai bata je gun Yaya Buhari ba. Wannan yasa tai ce "Ina zuwa!" Dakin yaa Buhari ta dosa, yana kwance ko alamar tashi bai yi ba. Kara tai masa a kunne da sauri ya mike a firgice. baya ta dan ja ta ce, "Ina kwana?" Ta fada tana ja da baya a hankali. Ganin ya mike yasa tai saurin fita a dakin tana dariya. Yaa Aslam dake tsaye yana jiran ta ya ga ta fito har ta sauka shima yabi bayan ta yana murmushi dan yasan tayi tsokanar da ta saba. A bakin mota ya ganta a tsaya budewa yayi ta shiga ya rufe sannan ya shiga bangaren sa. Tafiya suke a hankali suna hira abinsu. Har kofar department din su ya kai ta sannan ya kara mata kudi akan wanda Dady ya bata. Sallama yai mata ya ce, "Sai ya dawo daukar ta." Sai da ta ga tafiyar sa sannan ta nufi ajin daukar darasin su. Tana shiga taga Zainab zaune, karasawa tayi gun ta suka gaisa. Batai minti biyar da zuwa ba sai ga Sir Sabir nan ya shigo. Sanye yake da Milk din shadda ana mata aiki da milk din zare. Yayi kyau dashi. Kasa tayi da kanta tuna haduwar su jiya. Lectures yake musu da yayi tambaya zai yi pointing din ta. Tin tana jin kunya har ta sake tana bashi amsa. A haka suka gama lectures din. Da zai fita ya duka zai dauki wayar sa, yai mata magana a hankali cewar ta same shi a office. Wata faduwar gaba taji ta doke ta. A hankali ta daga kai ta kalle shi. Ita yake kalla saurin kawar da kan ta tayi tana wasa da yatsun ta. Waje ya fita. Wata ajiyar zuciya ta sauke, ita bata san hadin ta da malamin nan ba amman dai tana ji yana burge ta ko dan saukin kansa. Da kamar baza taje ba sai kuma ta ce da Zainab zataje ta dawo. Fita tayi ta nufi office din nashi jiki a sanyaye. Knocking tayi ya bata izinin shiga. Da sallama, ta shiga office din ta tsaya daga bakin kofa. Kallon sa tayi sau daya ta dauke idon ta. Yana zaune a kan kujera gaban sa, farfesun kifi ne da Doya da kwai. Kamshi ya cika office Din ci yake kamar baya son ci fuskar sa kuwa sai bata ta yake kamar mai cin magani. Kallonsa ya maida kan ta ya kasa dauke ido daga kallon ta. Yana son yarinyar nan amman bai san ta inda zai fara ba. Kawar da tunanin da yake yayi ya ce, "Zo nan!" Da kamar baza taje ba sai kuma ta dan matsa. Kallon ta ya kara yi ya rasa mene dalilin kiran nata. Kai ya dan shafa, ya ce, "Zo kici!" Kai ta girgiza ta ce, "Na koshi." Fuska ya bata, ya ce, "Zamu bata inda zan na baki abu kina kinci. Maza zo kici." Matsawa tayi ta zauna a kasa ba dan zata cin ba. Fulas din ya matsar mata dashi ya ce, "Bismillah!" Agogon hannun ta kalla sannan. Ta ce, "Zan je nayi Assignment fa." Ta yi maganar murya a shagwabe dan har ga Allah ta riga da ta saba da shagwaba in tana abu. bama in tana bukatar abu. Sabir kuwa jin muryar da take magana da ita yasa nan da nan tsigar jikin sa ta mike. *INDABAWA* [1/18, 14:17] Maryam S Indabawa🥰: *Asma'u Husnah* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* *Gidan Amanci da albarka* Dedicated to *My Lovelly Momy* *96-100* *KARE GIDA DA ALQUR'ANI DA ZIKIRAI DA SALLAH: Yana Daga Cikin Abinda Ke Taimakawa Wajen Tarbiyyantar da Yara Shine tsare Gidan Ta Hanyar Yawan Karatun Alqur'ani da Zakirai Musammam Zikiran Safe da Yamma Da Kuma Yin Sallolin Nafila a Cikin Gidan. Sabir kuwa a jin muryar da take magana da ita yasa nan da nan tsigar jikin sa ta mike. Idon sa ya kada yai ja, lumshe ido yayi ya bude, ya ce, "In in jiya da wa na ganki?" Yayi tambayar ba tare da yasan lokacin da ta fito ba. Kallon sa tayi ta ga ya canja amman bata kawo komai ba. Dan haka ta ce, "Ni da Yayanah ne!" Kai ya gyada kawai ya dauki waya yana dane dane. Kallon sa tayi ta kuma narke murya ta ce, "Naje?" Kallon ta ya tsaya yi, kafin ya ce, "Kunyi waya da Maryam!" Kai itama kawai ta gyada masa. A zahirin gaskiya baya son ta tafi ta bar shi amman dole ta tafi. Dan haka ya dinga mata tambayoyi. Sannan ya bata izinin tafiya. Tana tashi ya bita da kallo har ta fita ta rufo kofar idon sa na kan ta. Ido ya lumshe, yana me dafe zuciyar sa. Tana komawa ta bawa Zainab labarin abinda ya faru da yadda suka hadu jiya. Zainab dariya tayi ta ce, "Wai ke baki gane wani abu ba." Asma'u ta ce, "Me zan gane me ya faru?" Dariya kawai Zainab tayi ta ce, "Allah bazan fada miki ba. In kin gano ka zo kiban labari." Share maganar Asma'u tayi dan ta san Zainab akwai jan rai an kana son abu. Daga haka suka zauna aka shiga wani lecture din. Karfe hudu dai dai Yaa Aslam yazo, kiran Asma'u yayi bata dauka ba. Yasan tana massalaci. Dan haka ya fito ya zauna daga kasan bishiya. Yana zaune ya hango Sir Sabir ya taho a cikin motar sa. Kallon ssa yayi ya dan saki tsaki sannan ya dauke idon sa. Ya rasa dalili shi dai kawai gayen bai masa ba. Shima kuma ta bangaren Sir din ya ganshi sai dai shi a duk sanda suka hadu sai yaji wata faduwar gaba Yana zaune a haka Munasha ta gano shi. Gunsa ta nufa tana canja salon takun ta. A hankali ta karasa gun tai masa sallama. Dagowa yayi ya na kallon ta daga sama zuwa kasa. Ita kuma sai gyara tsayuwa take. Baki ya yamutse, kamar yaga kashi ya dauke kai. Wani iri taji amman duk da haka ta dake ta ce, "Sannu fa!" "Yauwah!" Ya fada kamar bai san wanda yai maganar ba dan kansa yana can kallon gefe. Zatai magana kenan ya daga mata hannu. Sannan ya mike ya tsaya a gaban ta. "Me kike nema ne?" Ya tambaye ta yana juya mata baya, Kallon sa ta tsaya yi tana hadiyar yawu. "Wallahi sai na dan dani zumar gayen nn." Ta fada a ranta. Tana kallon sa hadi da hadiyar yawu sai kace ta ga nama. "Uhmm uhmm daman!" Sai kuma tayi shiru. Murmushi yayi mai sauti sannan ya juyo gare ta. "Haba yan mata. Ki rike ajin ki na 'ya mace man. Nasan irin ku nasan kalar ku muna dasu daa yawa wadan da ke bibiyar mu. Ba wai son mu kuke haka kawai ba akwai wani abu a ranku. In da 'yar mutumci ce taga mutum tana son sa, ta san ta yadda zata tusa kanta gare shi har yasan da ita. Ba kamar ke da kikazo kika samen gaba da gaba ba. Kuma dan Allah kalli shigar ki. Wannan ba shigar ya'yan kirki bace, ko da zan so mace. Ba zan so macen da bata da kamun kai ba wacce ta gama tallata surar ta ga mazan waje ba." Shiru yayi sannan ya ce, "Kalle ki dan Allah kin kalli kan ki a mudubi kuwa kafin ki fito." Kanta take kalla sai a lokacin taga shirga dake jikin ta ba mai kyau ba. Kanta ya sha gashin doki har gadon baya, sannan ta saka riga da wando sun dame ta. Sai wani dan karamin mayafi da ta yafa ta saka takalmi mai tsini. Bilkis ce ta kara so gun ta ce, "Kai Munasha kina wuta fa." Shiru Maimuna tai mata, kallon su yayi ya ce, "Yanzu wannan dawa kikai koyi, kinsan wadan da kikai koyi dasu ko, to turawa ne, Bayan Allah madaukakin sarki ya ce, "Kada ku rike da al'adun yahudu da nasara kuma ya ce kada ku koyi abubuwan su wajen shiga sauya suna. Duk wanda ya jibanta al amaransa zuwa ga yahudu da nasara Allah (SWT) ya ce, ka zamto daga cikin su. Wato ya zamo su.' (Ma'ida 51) "Kinga ko anan kinyi abu nawa irin nasu. Ji shigar ki. ji wani suna da aka kira ki dashi. Manzon Allah (SAW) Yace, 'Duk wanda ya kwaikwayi wasu to shima ya zama shi.' Haka nan Manzon Allah (SAW) ya ce, 'Mutun na tashi ranar alkiyama da wanda yake so.' In kana son Allah da mazon sa kana yin abinda suka ce dasu zaka tashi. Haka nan in kana son wasun su, to da su zaka tashi. Haka nan aya ta 57 a cikin suratul ma'ida. Allah madaukakin sarki yaba cewa, "Yaku wadan da kukai imani karku riki wadan da suka rike adddinin mu da wasa da rudu' (yahudu da nasara) su ne suka rike addinin mu da wasa. Kar mu rike kafiri a cikin masoya (mudai dai yi mu'amala) muji tsoron Allah in mun kasance mumunai. kiji tsoron Allah ki koma ga Allah dan daga shigar ki ya nuna min ke wace, kada ki manta daman sai da shaidan ya ce, 'Wallahi sai ya samu rabon sa.' Wallahi ba kowa ke saka mana wadan nan ra'ayuyu kan ba in ba shi ba duk dan ya dulmiyar damu. Kiji tsoron Allah ki daina duk abinda kike. Duniya ba matabbaciyya bace, haka rayuwar mu a koda yaushe mai iya karewa ce." Ya juya kenan yaga Asma'u da Zainab suna tsaya suna sauraran su. Kuka Maimuna ta fashe da shi ta zube a kasa. Da sauri Asma'u ta karasa gun ta ta dago ta. Kallon Asma'u tayi idon tana fitar da kwalla. Kuka take sosai sai da kyar Asma'u ta lallashe ta tayi shiru. "Asma'u daman mutum kan hadu da mutum in Allah yaso. haduwa ta ga Aslam shine shiriya ta da izinin Allah. Nagode Yaa Aslam nagode insha Allahu bazan kara aikata abubuwan sabo ba." Sosai Yaa Aslam yaji dadi. "Ba komai. Kiji tsoron Allah dai a duk inda kike." Ya kalli Asma'u ya sakar mata murmushi. Zainab ya kalla ya ce, "A'ah In-low ashe kina nan." Murmushi tayi ta dan durkusa ta gaishe shi. Gaba sukai shi da ita suna hira. Har take basa labarin yadda Maimuna ta dinga damun Asma'u akan sa. Dariya yayi ya ce, "Allah sarki. Ita kuma me tayi." Zainab ta ce, "Ai kasan Asma'u in yan mutuncin suna nan akwai saukin kai." Sukai dariya gaba daya. Ya ce, "Lallai kam. Amman dadi na da Asma'u akwai hakuri sai dai in aka kai ta karshe basan ya zata yi ba kuma," "Wallahi kuwa ba ruwan kowa nata ne, kowa tana iya zama da shi. Allah Asma'u bata da temper kowa sai taka ta yadda zata saka farin ciki da karatun ya. Bata da abokin fada bata da riko." Murmushi yayi jin halayar Asma'u wanda shima ya san da su Asma'u tana can lallashin Maimuna har sai da ta ga ta daina kukan ta nutsu sannan sukai sallama. Bilkis kuwa duk da abinda Aslam ya fada ya ratsa ta amman bata jin zata daina abubuwan da take yi Gun Maimuna tayi ta ce, "Maunas......" Bata karasa fada ba ta dakatar da ita ta ce, "Bana son sunan nan ki kira ni da Maimuna in zaki iya" Ta mike tayi gun motar ta tashiga ta fita daga makarantar a guje. Baki Bilkis ta tabe ta shiga motar da Maimuna ta tabi bayan ta. Asma'u kam suna tsaye ita da Aslam da Zainab. Zainab na tsokanar ta da tini an kwace mata Yaa Aslam dinta. Duka ta kai mata ta ce, "Ai ba mai iya kwace shi sai Allah yaso." Yaa Aslam ya , "Allah ma bazai so na ni na kine ke kadai." Gira ta daga ta kalli Zainab ta ce, "Kinji ko?" Murmushi tayi tace, "Allah tabbatar da alheri." "Ameen!" Duk suka amsa sannan sukai sallama ta shiga motar gidan su itama suka shiga ita da Yaa Aslam suka tafi. A mota ma labarin yadda sukai da Maimuna ne yadda ya je gun ta a makaranta da lokacin da ta tambaye ta aikin sa da suna sa. Dariya take shi kuwa ya hade rai. Kallon sa tayi ta ce, "Me kuma nayi?" Motar ya faka a gefen hanya ya kalle ta ya ce, "Wai ke bakya kishi nane, daga nan baza ki gane me take nufi ba. Amman kin wani sake da ita." Murmushi tayi ta ce, "To Yaa Aslam ai sai mutum bai san matsayin sa a gun masoyin sa ba zai tsaya kishi. Ni da nasan ko da duk matan duniyar nan zaka aura sona daban ne a zuciyar ka haka nan kaunar da kake min baza ta taba tafiya ba kuma bame iya samun rabin ta daga wajen ka. Kada fa ka manta mukullin zuciyar ka nice. Tayya zan bude har wata ta shiga." Dariya yayi ya lakace hancin ta fe, "Ni dai ana kishi na dan baki san wasu mantan bane." Murmushi tayi ta ce, "Ina kishin ka man nafi kowa kishin ka da kishin masoyin sa saboda ni kadai nasan wane irin masoyi ne dani. Ina son ka. Ina kaunar ka bazan so wata ta rabe ka ba ni kadai nasan kishin da nake maka a cikin zuciya ta." *INDABAWA* [1/18, 14:17] Maryam S Indabawa🥰: *Asma'u Husnah* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* *Gidan Amanci da albarka* Dedicated to *My Lovelly Momy* *101-105* *KARATUN AL KUR'ANI A GIDA. Domin Karatun Alqur'ani Yanada Matukar Tasiri Wajen Bada Kariya Ga Shedanu a Gida. Sannan Yana Taimakawa Wurin Halartar Mala'iku Cikin Gidan Da Saukar Rahamar da Bata da Iyaka da Kuma Samar da Natsuwa da Yalwar Zuciya da Hutu ga Ma'abota Wannan Gida; Haka Shima Ambaton Allah (Zikiri) Duk Yana Haifar da Wannan Abubuwan.* Haka rayuwar Asma'u ta cigaba da tafiya cikin kwanciyyar hankali da samun soyayya daga wajen iyayen ta da masoyin ta kuma yayan ta. Cikin satin biyun da yazo yi ba karamin shakuwa ssuka kara ba. Kullum shi zai kai ta makaranta ya kuma dauko ta. Makarata sam ta daina yi dan haka kullum tana gaba da Sir Sabir ya shiga da ita yake yin tozali. Yanzu Maimuna ta shiryu dan gidan ta ma da motar da take hawa duk ta siyar ta fara business sosai take karatu tana kuma taimakawa iyayen ta. Dan duk karshen wata zataje gida. Haka duk zigar kawayen ta yan harka taki ta dauka. Dan har sam ta canja ta koma ga Allah kullum hijabai take sawa har kasa. Kasuwancin ta kuwa Allah yasa mata albarka dan a hostel duk abinda kake nema kaje gunta zaka samu banda kaya da take rabawa bashi da anyi albashi aba ta kudin ta. Sosai suke mutunci da Asma'u da Zainab. Suna kara koya mata abinda bata iya ba tinda ita lab science take karanta. Yau satin Yaa Aslam uku kenan a kano ya kasa komawa dan bai son ya tafi ya bar Asma'un sa. Suna zaune a garden kamar yadda suka saba in sun dawo gida da wuri. Aiki ya gama koya mata sannan ya kalle ta yai murmushi. "Lafiya?" ta tambaye shi. Murmushi ya kara. Fuska ta shagwabe ta ce, "Yaa Aslam Mene wai?" Dariya yayi. Sai ta bata fuska kuma. "Ayyah sorry yan mata na. Kinsan me?" Da sauri ta girgiza kai. Ya ce, "Wallahi kina yar karama na tuna lokacin da kullum kina saman cinya ta a zaune, ko bacci sai a guna zakiyi. Yanzu kuma kalle ki yadda kika girma kika zama mace." Sai yayi dariya. Fuska ta bata ta ce, "Allah Yaa Aslam din nan ko? Wai shekara nawa ma ka bani." Ido yayo waje dasu ya ce, "Tab! Allah yarinyar nan ko dan kinga ina kula ki ko?" "Kaji ka Yaya. Wai ina zaune a cinyar ka ko nai bacci a gun ka. Yanzu fa ka daina la'akari da da ma wallahi dan nasan ka gamai min wayoo ne kawai kaga yarinta ta." ta fada tana turo ba Dariya yayi ya ce, "Wallahi *Husnah* ke a autar ma ko ta karshe ce, rashin wayon ki rigimar ki ko?" Ya fada yana girgiza kai. Ya ce, "Dan ma Allah yasa na saba da wani zaki aura da na tausaya miki dan kafin ya saba da rigimar ki ko?" Murmushi tayi ta ce, "Shiyasa a ko da yaushe nake godewa Allah ya hadani da Yaya na. Yayan na ma wanda yafi so na. Wanda yafi kula dani wanda yasan komai nawa." Murmushi yayi ya ce, "Yarinya kin min wayoo nima zanje na samo wacce tasan ni." Fuska ta bata ta ce, "Akwai wace tasan ka ne sama dani. Kaga ni kanwar ka ce, zaka iya hukunta ni duk abinda nai maka Mami da Dady baza su ce komai ba. Amman kaje ka samo wacce mahaifin ta zai zo ya zane ka in ka taba masa 'yar sa." Dariya yayi ya ce, " *Husnah* kenan ina kaunar ki kaunar ki baza ta taba bari na ba. Da ita zan mutu." Asma'u ta ce, "Ya Aslam na maka alkawarin bazan taba barin ka ba zan kasance da kai a duk halin da kake ciki. Zan baka duk kan kulawa wacce ta rataya a kaina." Yaa Aslam ya ce, "Nima nayi miki alkawari...." Da sauri ta katse shi da "A'ah ni ba sai kayi ba." Ya ce, "Saboda me?" Ta ce, "Na yadda da kai zaka kula dani. Nasan ko ba aure a tsakanin mu zaka kula dani. haka kuma nasan zaka kasance dani. Wannan ma nasan zaka iya. Wanda zaka fada bana son yazo be faru ba shine kace baza kai min kishiya ba." Kallon ta yayi ya ce, " *Husnah* kenan baki yadda dani bane." Kai ta girgiza ta ce, "A'ah na yadda da kai. Ai ba mu san yadda Allah ya kaddara mana ba. Su wadan can nasan ko ba aure zamu kasance tare " Murmushi yayi ya ce, " *Husnah* Nai miki alkawari bazan guje miki. In dai soyayya tace kin gama samu, kuma insha Allahu babu kishiya." Murmushi tayi jikin ta a sanyaye ta ce, "Toh Ya Aslam. Amman ina tsoro wallahi." Ya ce, "Ki bar tsoro, ki sanya a ran ki za ayi auren mu. In Allah ya yadda zamuyi rayuwa, matsayin ma aurata za muyi shakuwa. Ba gudu ba ja da baya sonki zan tayi zan zauna dake har karshen rayuwa." Kanta ta sunkuyar ta ce, "Allah yasa." "Ameen!" Ya fada yana dago kanta. Murmushin yake tai masa. Fuska ya bata ya ce, " ki fadan damuwar ki?" Murmushi tayi ta ce, "Ina yawan jin faduwar gaba Yaa Aslam kuma nafi alakanta haka da soyayyar mu. Ya Aslam ina tsoro. Tsoro ma ba kadan ba." Murmushi yayi dan shima ta sanyayar masa da gwiwa. Ya ce, "Kinsa dai ki kadai ce a Cikin rai na ko? Wallahi *Husnah* ke kadai ce buri na da muradi na ban da burin samun wata mace in bake ba. filin zuciyata ko ta ina kece bake, ba sauran wajen da wata zata shigo shi to kwantar da hankalin ki." Fuska a dan marairai ce ta ce, "Kallon ka kadai nayi da ido nishadi yake sanya ni. Kai ne muradi na. farin ciki na abin alfahari na. Dole ina tsoron rasa ka da kai kadai na yadda na aminta da kai na fara soyayya dakai nake son kare ta in har na rasa ka ya kake zaton zan kasance." Ya ce, "Allah ma zai sa ke *tawa ce* " Ta ce, "Allah yasa." Ya ce, "Ameen!" Shiru sukai ya ce, "Kinsan me?" Kai ta girgiza masa. Ya ce, "Ina bude ido na farka a bacci ba wanda nake son na gani a dama na sai ke. Shi yasa da na tashi hoton ki shi nake fara kalla. Bana gajiya da kallon kyakyawar fuskar ki." Murmushi tayi ta ce, "Yaa Aslam ina rasa a cikin mu wa yafi son wani." Ya ce, "Kinsan me?" Ta ce, "A'ah!" Ya ce, "Ki bari sai munyi auren anan za a ga wanda yafi son wani. Ni dai nai alkwarain bazan taba saki kuka ba. zan ta faran ta miki zan kula dake insha Allahu." Dariya tayi ta ce, "Nima nai maka alkwaraiin kula da kai da sauke maka duk hakkin da ya hau kai na. Zan kasance mace ta gari me son farin cikin ka mai gusar maka da bakin cikin ka." Hannun ta ya kamo, ya ce, "Oya Alkawari." Dagowa tayi ta kalli cikin idon sa ta ce, "Nai maka alkawarin bazan taba daina son ka ba. Kuma zan kasamce mace ta gari a tare da kai kuma bazan taba guje maka ba." Murmushi yayi ya ce, "Nima na miki alkawarin bazan taba guje miki ba haka nan zan ta son ki har karshen rayuwa ta zan kasance mai saki farin cikin ki." "Allah yasa." ta ce, Ya amsa da "Ameen!" Ta ce, "Yaa Aslam duk abinda nake aka ce kai ko sai na saurare shi." Murmushi yayi ya ce, "Bajin dadin labari in ba naki ba, ba shauki ke ko acikin taurari kin yi daban. Kaunar ki nake yi kullum a cikin zuciya ta." "Hmm Ya Aslam! Kenan" " *Husnah* komai nawa naki ne ban da burin da ya wuce naki. Kume naki burgeni yake yi. Surar ki tamkar ke kika tsara ta ina matukar kaunar ki." Ido ta rufe da hannayen ta. Hannun nata ya kamo ya ce, "Dan Allah kalli yatsun ki abin sha'awa." Janye hannun ta tayi da sauri. Fuskar ta ya kalla ya ce, "Kalli fuskar ki me kyau." Ido ta bude ta kalle shi. Ya ce, "Kalli idanun ki masu kyau da girma da birkita tunani. Ina kunar su." Baki ta dan turo, ya ce, "Ya salam ai sai kisa nayi abinda ban shirya ba. Ina son bakin nan naki." Kafa ta buga a kasa ta ce, "Kai Yaa Aslam!" Dariya yayi ya ce, "Wallahi komai naki burge ni yake. Komai. komai nake nufi." Mikewa tayi ta ce, "Ni mu shiga ciki magariba ta taho." Mikewa yayi ya bi bayan ta rike da littatafn ta. Suna shiga ta haye sama dakin ta. Kan gado ta fada ta lumshe ido. Dakin ya shiga ya ajiye mata littafan sannan ya kuma gefen ta yana kallon ta. Jin ido na bin ta, ya sa tai ssaurin bude ganin shi tayi a gaban ta ya tsura mata ido. Mikewa tayi zaune ta ce, "Ya dai?" Murmushi yayi ya mike ya ce, "Ji kiran sallah amman kika zo kika kwanta ko? Ko bakya yi ne?" Kai ta gyada masa, mikewa yayi ya ce, "Bari nai alwala." Ya shiga bandakin ta. Alwala yayi ya fito ya ce, "To na tafi sallah. Ya kamata kiyi lazumi ko ki karanta alkur'ani tinda ba sallah zakiyi ba." Kai ta gyada masa. Dan ya saba sanin in ba yin sallah take ba. Ita wani lokacin tana daukar sa tamkar Yaa Buharin ta ne. *INDABAWA* [1/18, 14:18] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* *Gidan Amanci da albarka* *Gaskiya ina jin dadin yadda kuke kkokari wajen zaman lafiya da kula da juna. Ina gaishe lu yan kungiyar mu. Allah kara muki basira da daukaka.* Dedicated to *My Lovelly Momy* *106 - 110* *Karanta Alkur'ani a gida* *Yana Daga Cikin Dalilan Dake Nuna Haka Hadisin *Abi-Hurairah (ra)* Inda *Manzon Allah(ﷺ)* Yake Cewa:_ *{ﻋَﻦْ ﺃَﺑِﻲ ﻫُﺮَﻳْﺮَﺓَ ﺃَﻥَّ ﺭَﺳُﻮﻝَ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﺻَﻠَّﻰ ﺍﻟﻠَّﻬﻢ ﻋَﻠَﻴْﻪِ ﻭَﺳَﻠَّﻢَ ﻗَﺎﻝَ ﻟَﺎ ﺗَﺠْﻌَﻠُﻮﺍ ﺑُﻴُﻮﺗَﻜُﻢْ ﻣَﻘَﺎﺑِﺮَ ﺇِﻥَّ ﺍﻟﺸَّﻴْﻄَﺎﻥَ ﻳَﻨْﻔِﺮُ ﻣِﻦَ ﺍﻟْﺒَﻴْﺖِ ﺍﻟَّﺬِﻱ ﺗُﻘْﺮَﺃُ ﻓِﻴﻪِ ﺳُﻮﺭَﺓُ ﺍﻟْﺒَﻘَﺮَﺓِ [مسلم:٧٨٠]}* '''Fassara:''' _An Kar6o Daga *Abi-Hurairah (ra)* Yace *Manzon Allah(ﷺ)* Yana Cewa: *"Kada Ku Mayar da Gidajenku Kamar Makabartu, Lallai Shedan Yana Gudu Daga Gidan da Aka Karanta Suratul Baqara a Cikinsa".* (Muslim: 780)_ *Lallai karata Suratul bakara a ggida yana da amfani. Dan akwau wata Mamanah in ta saka a gida har tsorata ta ake. Da ta tambayi wani malami ya ce ta cigaba da sakawa insha Allahu ta daina gani.* *Ko kunsan cewa in da wani sihiri a tare da kai ko al jannu karanta suratul bakara ko saka karatun ta yana baka kariya.* *Mu daure da karanta ta ko da aya kadan ke daga ciki* *Mu daure da son karanta alkur'ani* Watan Yaa Aslam daya ya fara shirin tafiya. Asma'u ji tayi kamar me, dan kuka ta sha shi tinda ya ce mata zzai tafi. Ranar Asabar ya saka tafiyar tashi. Ranar juma'a ya dauke ta ya kai ta shopping yai mata siyayya mai yawan gaske. Amman duk jikin ta a sanyaye yake da ka kalle ta zaka san bata da walwala. Haka suka dawo gida duk yadda yaso ta sake kasawa tayi sai dai ta dan yi masa murmushin yake. Da dare bayan sun ci abinci ta shiga dakin sa dan taya shi hada kaya. Shima yana kwance ya fito da kayan ya ajiye akan gado. Tunanin shima rabuwa da ita yake. Kallon sa tayi ta wuce wajen kayan ta fara zuba masa a cikin akwatin sa. Motsin ta da yaji shi ya sa shi bude idon sa. Kallon ta ya tsaya yi hada masa kayan take cikin sanyin jiki. Jin idon sa akan ta yasa ta kalle shi, Murmushi ta sakar masa, ta cigaba da abinda taken. Mikewa yayi zaune ya zura mata ido. Ko kiftawa baya yi. Har ta gama bai dauke idon sa daga kallon ta ba. Takalman sa ta fara hadawa ta gama ta koma gefen sa ta zauna. Kallon sa ya dawo da shi kan ta, murmushi ta kara sakar masa. "Yaya nah lafiya?" Ta tambaye shi. "Baby nah bana son ganin ki a damuwa," Ya fada yana kamo hannun ta. Hannun ta. ta zare ta ce, "Yaya nah naji sai kuma me?" "Bansan menene ba. Amman bana son barin ki Asma'u bana son nima na tafi. Ki yadda nayi magana ai mana auren kinji." Kasa tayi da kanta sannan ta ce, "To Yaya nah yanzu in mukai auren karatu na fa. Kaga nazo gangara ka bari nan da wata shekara sai muyi aure ko?" Kai ya gyada ya ce, "Haka ne, amman bana son na rasa ki bana son nayi nesa da ke." "Haba Yaya nah kar ka manta fa dazu kai ka gama lallashi na akan nayi hakuri muna tare ko?" Hannun ta ya kamo ya matse shi a cikin nasa. Ido ya lumshe, sannan ya bude. Kallon ta ya tsaya yi tin tana kallon cikin idon sa, har ta gaza kalla dan wani abu take ganin yana shiga cikin nata. Lumshe idon tayi matsowa yayi kusa da ita. Ya ce, "Asma'u ki riken Alkawari na kar ki taba bari na in dai ina cikin duniyar nan ina son ki yi min alkawarin ke tawa ce." Idon ta, ta bude wanda suka canja kala zuwa ja, ta ce, "Wallahi Yaa Aslam na maka wannan alkawarin bazan taba barin ka ba. Sai dai in kai ka bukata." Ido ya lumshe samnan ya ce, "Ni kuwa tayaya za'ai na bukaci rabuwa da rayuwa ta." Murmushi tayi ta ce, "Bare kuma ni." Yayi murmushi. "Bari naje na kwanta!" Kallon ta yayi ya ce, "Kamar mu kwana tare." Murmushi tayi ta ce, "Allah kawo ranar da zamu kwana taren." "Ameen!" Ya fada yana mikewa. A kofar dakin ta suka kara tsayawa sun dauki kusan minti ashirin suna tsaye sannan sukai sallama ta shiga. Tana shiga daki ta fashe da kuka. Rasa kukan me take tayi amman ta san cewa ba zai rasa nasava da tafiyar Yaa Aslam ba. Sai da taji kiran sa a waya sannan tai saurin shiga bayi tai wanka ta fito ta shirya sanann ta kira sa. "Baby na kin kwanta ne?" Ya tambaya daga can site din. "Eh yanzu na kwanta." ta bashi amsa. Ya ce, "To kiyi addu"a sai da safe." Ta ce, "Allah tashe mu lafiya." Ta fada tana kashe wayar. Washe gari tin asuba ta tashi ta yi duk abinda zata yi. Wanka tayi ta koma gado tai kwanciyyar ta. Sai karfe sha biyu sannan ta mike ta kara watsa ruwa ta shirya cikin wani tissue pink material wanda akai mata dinkin fitetgown, batai kwalliya ba. Hoda da man lebe kawai ta shafa sai kwalli da ta saka a idon ta. Falo ta fito ba kowa a sama a kasa ta dinga jin maganar su. Sauka tayi a hankali ba ta kalle su ba sai da ta shiga kkitchen. Ruwan zafi kawai ta hada ta fito falo. Sai da ta gaishe da Yaa Aslam da Yaa Buhari sannan ta nufi daining. Zama tayi ta kasa shan tea din ma. Yaa Aslam ne ya mike ya shiga kitchen ya dafa mata indomie sai ya soya mata kwai. Daining ya nufa ya zauna a kujerar dake facing tata. Kallon sa tayi ta sakar masa murmushi. Plate din hannun sa ya tura mata gaban ta. Ya daga mata gira alamar 'ta ci.' Ja tayi ta saka spoon tana ta wasa da shi. Amsar spoon din yayi ya fara bata a baki. A hankali a hankali har ta ci mai yawa sannan ta ce ta koshi. Falo suka koma suna hira da Yaa buhari ita kuwa tai shiru sai dai ta kalli.wannan ta kalli wannan. Kiran sallah aka yi wannan yasa kowa ya tafi dakin sa. Alwala su Yaa Aslam sukai suka wuce massalaci. Ita kuma a daki tai sallar tinda ta idar ta kasa tashi daga inda take har karfe biyu tana zaune. Yaa Aslam ne ya shigo dakin cikin shirin tafiyar sa. Yana sanye da Milk din wando sai maroon kalar riga mai dogon hannu. Takalmin kafar sa ma maroon ne. sai tashin kamshi yake. Tana ganin sa ta mike ta saki fara'a shima murmushin yayi ya kamo hannun ta suka fito. Mami na falo suka tadda ta. Sallama yai mata suka fice tare. Yaa Buhari ta gani a cikin mota yana jiran su. Bayan mota suka shiga daga ita har shi har lokacin hannun ta na cikin nasa. Wata zoben azurfa ya fito dashi daga cikin jakar sa. Ya zura mata a yatsan ta take hannun ya kara gaske yai mata kyau. Sumbatar hannun yayi yana kallon cikin idon ta. Lumshe idon tayi tana mai yin murmushi. Suna zuwa airport din Yaa Buhari ya fita a motar. Kallon ta yayi ya ce, "Baby na zan tafi ki kular min da alkawari na." Asma'u Ta ce, "To Yaya nah Allah kiyaye hanya, kar ka manta da alkawari na nima kaji." Ya ce, "Insha Alalhu bazan manta ba!" Yai mata kiss a goshi sannan ya fita. Ta taga ya leko ya ce, "Ki zauna ba sai kin ffito ba. Kai ta daga masa sai kuka kuma. Kuka sosai take ba shiri ya koma cikin motar ya jata jikin sa yana lallashin ta. Amman kamar kara zuga ta yake. Ya jima yana lallashin ta da kalamai masu sanyaya rai yaji ta daina kuka. Bai daina shafa mata bayan ta ba da kwantar da hankalin ta. Sai da ya dauki minti goma a haka sannan ya dago dan ya ga me take. Bacci yaga tana yi sai ajiyar zuciya take saukewa. Murmushi yayi ya kwantar da ita sannan ya kara kissing nata a goshi. Waya ya dauko ya dauki pics din ta sannan ya fita a hankali. Yaa Buhari ya gani suka karasa ciki. Basu jina ba ya tashi. Dawowa mota Yaa Buhari yayi ya ganta tana ta baccin ta. Motar ya tayar suka tafi gida a hankali yake tukin duk dan kar ya tashe ta. Yana tausaya musu yana musu addu'a akan Allah ya mallaka musu juna su. Dan son da sukewa juna su shi gani yake kamar yayi yawa. Kuma yana tausaya musu dan kar wani a bu ya faru bai san wane hali zasu shiga ba. Har ya isa gida bata tashi ba. Daukar ta yayi ya kaita dakinta samman ya sanar da Mami sun dawo. Sai magariba ta tashi. Tana bude ido taji idon ta a kumbure. Taba su tayi sai kuma ta tuna da abinda ya faru dazu. Wani kukan ta kuma saki ita kadai tayi iya yin ta sannan ta mike ta shiga ban daki. Wanka tayi tayo alwala ta fito ta saka kayan bacci ta tada sallah tana idar wa ta kwanta anan inda take Wani bacci ya kuma sace ta. Sai tara saura ta farka. Bandaki ta shiga tai alwala ta fito tai sallah zata hau gado kenan sai ga Mami da Dady nan sun shigo. Mami rike da katon tire a hannu. Gefen ta Dady ya zauna ya ce, "Wannan shakuwar taku Asma'u tayi yawa. Yanzu inda Yayan naki yai aure ai sai Antyn ki tana jin haushi kiyi hakuri da kin gama karatu zaki je ki musu hutu kinji." Kai ta daga tana masa murmushi sannan tai masa sannu da zuwa. Abinci Mami ta zuba mata sai da ta ga taci ta koshi sannan suka fita daga daki Kan gado ta koma ta kwanta kiran sa ne ya shigo. Dagawa tayi cikin sanyin murya. Ta ce, "Yaya nah ka isa lafiya yasu Momy da Dady?" "Duk suna lafiya ya na baro ku?" "Lafiya Alhamdulilah." "Wallahi ina kewar Baby na." Murmushi tayi ta ce. "Nima haka." Daga haka suka fara hirar su kamar yadda suka saba. Sun jima suna hira sannan sukai sallama kowa ya kwanta. *Uhmmm* *INDABAWA* [1/18, 14:19] Maryam S Indabawa🥰: *Asma'u Husnah* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* *Gidan Amanci da albarka* Dedicated to *My Lovelly Momy* Allah kara budi Allah ya daukaki. Ameen. *111-115* _Har Wayau An Kar6o Hadisi Ingantacce Daga *Jabir (ra)* Yace Yaji *Manzon Allah(ﷺ)* Yana Cewa:_ *{ﻋَﻦْ ﺟَﺎﺑِﺮِ ﺑْﻦِ ﻋَﺒْﺪِ ﺍﻟﻠَّﻪِ ، ﺳَﻤِﻊَ ﺍﻟﻨَّﺒِﻲَّ ﺻَﻠَّﻰ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻋَﻠَﻴْﻪِ ﻭَﺳَﻠَّﻢَ , ﻳَﻘُﻮﻝُ : " ﺇِﺫَﺍ ﺩَﺧَﻞَ ﺍﻟﺮَّﺟُﻞُ ﺑَﻴْﺘَﻪُ ﻓَﺬَﻛَﺮَ ﺍﻟﻠَّﻪَ ﻋِﻨْﺪَ ﺩُﺧُﻮﻟِﻪِ ﻭَﻋِﻨْﺪَ ﻃَﻌَﺎﻣِﻪِ , ﻗَﺎﻝَ ﺍﻟﺸَّﻴْﻄَﺎﻥُ : ﻻ ﻣَﺒِﻴﺖَ ﻟَﻜُﻢْ ﻭَﻻ ﻋَﺸَﺎﺀَ ، ﻭَﺇِﺫَﺍ ﺩَﺧَﻞَ ﻓَﻠَﻢْ ﻳَﺬْﻛُﺮِ ﺍﻟﻠَّﻪَ ﻋِﻨْﺪَ ﺩُﺧُﻮﻟِﻪِ , ﻗَﺎﻝَ ﺍﻟﺸَّﻴْﻄَﺎﻥُ : ﺃَﺩْﺭَﻛْﺘُﻢُ ﺍﻟْﻤَﺒِﻴﺖَ ، ﻭَﺇِﺫَﺍ ﻟَﻢْ ﻳَﺬْﻛُﺮِ ﺍﻟﻠَّﻪَ ﻋِﻨْﺪَ ﻃَﻌَﺎﻣِﻪِ , ﻗَﺎﻝَ : ﺃَﺩْﺭَﻛْﺘُﻢُ ﺍﻟْﻤَﺒِﻴﺖَ ﻭَﺍﻟْﻌَﺸَﺎﺀَ [مسلم:٢٠١٨]}* '''Fassara:''' _An Kar6o Daga *Jabir bn Abdullah (ra)* Yace: Naji *Manzon Allah(ﷺ)* Yana Cewa: *"Idan Mutum Zai Shiga Gidansa Sai Ya Ambaci Allah Yayin Shigansa, da Kuma Lokacin da Zaici Abinci, Sai Shaidanu Suce (da 'Yan Uwansu Shaidanu): Baku da Wurin Kwana Kuma Baku da Abincin Dare. Idan Kuma Ya Shiga Gidan Be Ambaci Allah Ba a Yayin Shigansa, Sai Shaidan Yace (da Yan Uwansa Shedanu): Kun Samu Wurin Kwana. Idan Kuma Be Ambaci Allah ba Yayin Cin Abinci, Sai Shaidan Yace da Yan Uwansa Kun Samu Wurin Kwana da Abincin Dare".* (Muslim) Haka rayuwa ta cigaba dan gashi har Asma'u sun fara exam. Murna suke dan baza su dawo skul ba asibiti zasu tafi su zama student doctor. Sun gama Exam lafiya. Inda suka koma gida suna shan hutun su. Dady kuwa har ya dawo an gama hada mata asibitin ta. Bangaren Yaa Aslam kuwa sai wata kulawa da ya dada bata. Dan shakuwar su ta koma yawa yanzu haka ma zai zo wani aiki zai yi sati daya a kano. Murna gun Asma'u kamar me? ************ Bangaren Sabir kuwa, duk ya damu bama da akai hutun nan baya samun damar ganin Asma'u. Mamah ta rasa me yake damun sa dan ba karamin sauyawa yayi. Duk yadda Mamah taso ya fada mata damuwar sa ki yayi sai dai ya ce ba komai. Zaune yake akan kujera dake garden din gidan su. Idonsa a lunshe sai sake saken yadda zai ga Asma'u yake. Can ya mike zaune da sauri yana lalubar number wayar Maryam. Kira yayi sai da ta daga suka gaisa sannan ya ce, "Daughter number wayar *Husnah* nake son ki bani." "Ohk bari na turo maka." Ta katse wayar tana murna dan tin da taga Asma'u taji tai wa Uncle din ta sha'awar ta. Nan da nan ta tura masa, tana addu'ar Allah yasa ta zama matar sa. Yana ganin number yai saving din ta da. *My Hussy* Ya jima yana kallon sunan sannan ya tafi kira. Tana tafiya zai yi sauri ya katse kiran. Yayi haka fin sau goma sannan ya hakura dan ya rasa me zai ce mata in ta dau wayar. Ya jima yana tunanin abinda zai ce mata. Sako ya tura mata da wani sabon sim din sa. sannan ya ajiye wayar. Can kuma ya dau wayar ya shiga whatsapp din sa. Searching sunan ta yayi sai gashi yayi appearing. Nan da nan ya shiga ciki. Last seen nata bata dade da sauka ba. Profile picture din ta ya bude, Hoton Asma'un ya gani tana tsaye a garden din su. Sanye take da wata jar doguwar riga tayi rolling da bakin mayafi. Hannun ta rike da waya fuskar ta ba makeup amman tayi kyau tana murmushi dimple din ta ya lotsa. Ba karamin kyau tayi ba, da sauri yai saving hoton sannan ya kura mata ido. Kasa dauke idon sa yayi daga kallon hoton. Ido ya lumshe, Sannan ya bude ya saki wani murmushi. Mikewa yayi ya shige cikin gidan. Wanka yayi ya shirya cikin Blue din shadda, ba karamin kyau yayi ba. Mikewa yayi ya fita. Mamah ya gani a falo. Karasa wa yayi ya ce, "Mamah zan fita." Kallon sa tayi taga ya canja cikin lokaci kadan. Kallon sa tayi ta ce, "To a dawo lafiya." "Ameen!" ya asma ya fita. Kallo Mamah tabi shi da shi har ya fice. Shoprite ya nufa kai tsaye daga gida. Ciki ya shiga, ya fara shopping hankalin sa kwance. Kamar daga sama ya hango ta tana dibar kaya ita ma, Ido ya goge ya ga da gaske dai ita din ce. Tsayawa yayi da dibar kayan ya dinga binta da kallo. Sanye take da Ash kalar doguwar riga, sai bakin mayafi da ta yafa da jaka da takalmi duk bakake. Binta ya dinga yi da kallo har ta gama tayi wajen biya. Da sauri shima yayi gun. Yana zuwa ta karasa itama. ATM card din sa ya mika aka zara, juyowar da zai yi suka hada ido. Da sauri tai kasa da kai, ta dan durkusa ta ce, "Sir Ina yini?" Kallon ta ya dan karayi ya amsa da "Lafiya lou, ya hutu." "Alhamdulilah!" Ta bada amsa kan ta a kasa. "Masha Allah. Bayar a lisaafa miki." Mikawa tayi ya tsaya yana jiran a gama ya biya. Anan gamawa ya mika masa card din sa ya ce, ya dauka a ciki. Kallon sa Asma'u tayi ta ce, "Lah Sir da kudi aguna." Kallon ta yayi ya ce, "Ai na sani. Na dai biya miki ne kawai." Dan durkusa wa tayi ta ce, "Nagode!" Daukar mata ledar yayi ya dauki tashi suka fita. A Napep take dan haka ta ce, fita zatayi zata hau mota. "Muje na rage miki hanya." Ya fada yana yin wajen motar sa. Ba dan taso ba tabi bayan sa. Shi ya bude mata mazaunin ta sannan ya koma ya shiga bangaren sa. Motar ya tayar suka fita sannan ya dan kalle ta ya ce, "Ina zamuyi?" "Jan bulo. 3rd gate wajen forestry." kai ya gyada suka dau hanya. A hankali suke tafiya kamar baya son tukin duk dan kar su rabu. Kallon ta ya danyi yaga hankalin ta na kan Wayar ta da take dannawa. Kai ya dauke ya cigaba da tuki. Kiran ta akai ta daga tana satar kallon sa tayi sannan ta dauka. A hankali tayi sallama, daga dayan bangaren ya Amsa. "Baby nah kina ina ne?" Dan taga missed din sa ganin suna tare da Sir Sabir ne ya sa bata kira sa bba. "Naje shoprite ne, ya kake ya aiki?" Ta tambaye shi. "Lafiya Alhamdulilah! Me da me kika siyo?" "Uhmm in naje gida zan nuna maka su." "Ok sai kin dawo. Ki kular min da kan ki." "To nima ka......." Sai kuma tayi shiru. Ganin Sabir na kallonta. Kasa tayi da kanta ta ce, "Sai na koma" Ta katse wayar. Sabir kuwa jin tana waya da namiji ba karamin tada masa da hankali yayi ba. Har suka je unguwar ta nuna masa layin sannan suka karasa kofar gidan. Horn yayi mai gadi ya bude masa gate suka shiga. Mami suka gani zaune a barander dake kofar falo. Fitowa tayi tai masa godiya. Kallon wajen da Mami tayi ta ce, "Kazo ku gaisa da Mami." "Ok!" Ya fada yana fitowa. A hankali cikin nutsuwa suka karasa wajen da Mami take. Suna zuwa ya durkusa ya gaishe da Mami. Bayan sun gaisa ne, Asma'u ta ce, "Mami wannan shine Sir Sabir lecturer mu ne, mun hadu a shoptite kinga shi ya biya min kudin siyayya ta ma ya rage min hanya kuma." Kai Mami ta gyada ta ce, "Kai Sabir har da wahala haka. Angode to Allah saka da alheri " Asma'u ta kalla ta ce, "Ki kawo masa lemo man." "A'ah Mami wallahi Alhamdulilah." yai maganar kan sa a kasa dan kunyar Mami yake ji sosai. "A'ah Sabir kar muyi hka da kai." Ta kalli Asma'u ta ce, "Je ki dauko masa." Mikewa Asma'u tayi tayi cikin gida. Bata jima ba ta dawo rike da 5alive na kwali sai kofi a hannun ta da plate da ta zubo cake a ciki. Ajiyewa tayi akan table din dake wajen. Mikewa mami tayi ta ce, "Ka saki jiki kaci kaji." Tayi cikin gidan. Zama Asma'u tayi akan kujera ta nuna masa dayar ta ce, "Bismillah!" Mikewa yayi ya zauna ta zuba masa lemo. Lemon kadai ya sha sanna ya mike ya ce, zai tafi. Har cikin falo ta raka sa yayi wa Mami sallama sannan suka fito har bakin mota ta raka shi. Sabir kuwa sosai yaji dadin irin tarbar da Mami tai masa. Sosai ya dinga murna dan ya ga gidan su Asma'u. Da haka ya tafi gida ransa kamar takarda dan farin ciki. Yana komawa ya zauna a falon suka dinga hira da Mamah. Mamah dai sai mamakin canjin sa take dan ya jima bai zauna sun yi hira kamar haka ba. Suna zaune Abbi ya dawo. Nan suka zauna suna ta hira har akai sallah magariba suka je sukai sallah suka dawo. A falo suka zauna suka ci abinci sannan suka ci gaba da hira har lokacin baccin su yayi suka mike suka yi dakin nan su. Yana shiga daki ya tura mata da sakon sai da safe da kalamai masu dadi. Ban daki ya shiga yayi wanka ya fito ya haye gadon sa. Online ya hau ya dinga kallon ta a online amman ya kasai mata magana. Haka ya shiga gallery ya maida hoton ta kamar TV. Da shi yayi bacci. *INDABAWA* [1/18, 14:19] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* *Gidan Amanci da albarka* Dedicated to *My Lovelly Momy* *116-120* AN Ruwaito a Cikin Littafin Ibn-Sunni, da Sanadi Me Rauni, Daga *Abi-Sa'eedil Khudry (ra)* Yace: *Manzon Allah(ﷺ)* Ya Kasance Idan Rana Ta Fito Yana Cewa:_ *{ﺍﻟَﺤْﻤَﺪُ ﻟِﻠَّﻪ ﺍﻟَّﺬِﻱ ﺟَﻠَّﻠَﻨَﺎ ﺍﻟْﻴَﻮْﻡَ ﻋَﺎﻓِﻴَﺘَﻪُ ، ﻭَﺟَﺎﺀَﻧَﺎ ﺑِﺎﻟﺸَّﻤْﺲِ ﻣِﻦْ ﻣَﻄْﻠَﻌِﻬَﺎ ، ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺇِﻧِّﻲ ﺃَﺻْﺒَﺤْﺖُ ﺃَﺷْﻬَﺪُ ﻟَﻚَ ﺑِﻤَﺎ ﺷَﻬِﺪْﺗَﻪُ ﻋَﻠَﻰ ﻧَﻔْﺴِﻚَ ، ﻭَﺷَﻬِﺪَﺕْ ﺑِﻪِ ﻣَﻼﺋِﻜَﺘُﻚَ ﻭَﺣَﻤَﻠَﺔُ ﻋَﺮْﺷِﻚَ ﻭَﺟَﻤِﻴﻊُ ﺧَﻠْﻘِﻚَ ﺃَﻧَّﻪُ ﺃَﻧْﺖَ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺍﻟَّﺬِﻱ ﻻ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻ ﺃَﻧْﺖَ ﻗَﺎﺋِﻤًﺎ ﺑِﺎﻟْﻘِﺴْﻂِ ، ﻻ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻ ﺃَﻧْﺖَ ﺍﻟْﻌَﺰِﻳﺰُ ﺍﻟْﺤَﻜِﻴﻢُ ، ﺷَﻬَﺎﺩَﺗِﻲ ﻣَﻊَ ﺷَﻬَﺎﺩَﺓِ ﻣَﻼﺋِﻜَﺘِﻚَ ﻭَﺃُﻭﻟِﻲ ﺍﻟْﻌِﻠْﻢِ ﻭَﻣَﻦْ ﻟَﻢْ ﻳَﺸْﻬَﺪْ ﺑِﻤِﺜْﻞِ ﻣَﺎ ﺷَﻬِﺪْﺕُ ، ﻓَﺎﻛْﺘُﺐْ ﺷَﻬَﺎﺩَﺗِﻲ ﻣَﻜَﺎﻥَ ﺷَﻬَﺎﺩَﺗِﻪِ ، ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺃَﻧْﺖَ ﺍﻟﺴَّﻼﻡُ ﻭَﻣِﻨْﻚَ ﺍﻟﺴَّﻼﻡُ ﻭَﺇِﻟَﻴْﻚَ ﻳَﺮْﺟِﻊُ ﺍﻟﺴَّﻼﻡُ ، ﺃَﺳْﺄَﻟُﻚَ ﻳَﺎ ﺫَﺍ ﺍﻟْﺠَﻼﻝِ ﻭَﺍﻹِﻛْﺮَﺍﻡِ ﺃَﻥْ ﺗَﺴْﺘَﺠِﻴﺐَ ﻟَﻨَﺎ ﺩَﻋْﻮَﺗَﻨَﺎ ، ﻭَﺃَﻥْ ﺗُﻌْﻄِﻴﻨَﺎ ﺭَﻏْﺒَﺘَﻨَﺎ ، ﻭَﺃَﻥْ ﺗَﺰِﻳﺪَﻧَﺎ ﻓَﻮْﻕَ ﺭَﻏْﺒَﺘِﻨَﺎ ، ﻭَﺃَﻥْ ﺗُﻐْﻨِﻴﻨَﺎ ﻋَﻤَّﻦْ ﺃَﻏْﻨَﻴْﺘَﻪُ ﻋَﻨَّﺎ ﻣِﻦْ ﺧَﻠْﻘِﻚَ ، ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺃَﺻْﻠِﺢْ ﻟِﻲ ﺩُﻧْﻴَﺎﻱَ ﺍﻟَّﺘِﻲ ﻓِﻴﻬَﺎ ﻣَﻌِﻴﺸَﺘِﻲ ، ﻭَﺃَﺻْﻠِﺢْ ﻟِﻲ ﺩِﻳﻨِﻲ ﺍﻟَّﺬِﻱ ﻫُﻮَ ﻋِﺼْﻤَﺔُ ﺃَﻣْﺮِﻱ ، ﻭَﺃَﺻْﻠِﺢْ ﻟِﻲ ﺁﺧِﺮَﺗِﻲ ﺍﻟَّﺘِﻲ ﻓِﻴﻬَﺎ ﻣُﻨْﻘَﻠَﺒِﻲ}* _*"Alhamdulillahil Lazi Jallalanal Yauma Ãfiyatahu, Wa Jã'a Bish Shamsi, Min Ma'dli'aha, Allãhumma Asbahtu Ash'hadu Laka Bimã Shahidta Bihi Li Nafsika, Wa Shahidat Bihi Malã'ikatuka Wa Hamalatu Arshika Wa Jami'a Khalqika, Innaka Antallahu Lã'ilaha Illã Antal Qa'imu Bil Qisdi, Lã'ilãha Illã Antal Azizul Hakeem, Aktub Shahãdaty Ba'ada Shahãdati Malã'ikatika Wa Ulul Ilmi. Allãhumma Antass Salãm wa Minkas Salãm Wa Ilaikas Salãm, As'aluka Yã Zal-Jalãli Wal Ikrãm An Tastajiba Lanã Da'awatana, Wa An Tu'u'diyanã Ragbatanã, Wa An Tu'u'diyana Amman Agnaitahu Annã Min Khalqika. Allãhumma Aslihli Deeni Allazi Huwa Ismati Amri, Wa Aslihli Dunyayal Laty Feeha Ma'ashy, Wa Aslihly Ãkhiraty Allaty Ilaihã Munqalaby".¹*_ Asma'u kuwa tana komawa ciki ta hau daukar kayan da ta siyo tana nunawa Yaa Aslam. Hiran suka sha sannan ta mike tayi alwala. Aslam ganin karatun su Asma'u yazo gangara ya sa yayi takakiya yazo har kano. Asma'u bata san da zuwan sa ba. Sai da ta dawo daga gidan su Zainab sannan ta ganshi. Murna kamar me taji dadin ganin sa. Daki ta shiga danyin wanka. Amman tindata fito vata sake ganin sa ba. Sai da su Dady ta ganshi da ta sauko da akai sallah isha'i. Sai kus kus taga suna yi da Dady wannan yasa ma batayi wajen su ba. Tare duk suka ci abinci, suna gamawa tayi dakin ganin akwai maganar da suke da Dady. Tana shiga dakintai wanka ta haye gado. faduwar gaba taji tana yi, da haka har bacci ya dauke ta. Can cikin bacci taji karar wayar ta. Mikewa tayi tana salatin annabi. sannan ta dauko wayar. Number Yaa Aslam ce. Dauka tayi cikin sanyin murya ta masu bacci. "Baby na har kinyi bacci?" Ya tambaye ta. Kai ta gyda masa ta ce, "Eh kai fa?" Ya ce, "Yanzu dai zan kwanta na ce bari naji ya Baby na take." Murmushi tayi ta ce, "Ina lafiya " "To sai da safe ko?" Kai ta gyada nasa ta ce, "Allah tashe mu lafiya. " Ta kashe wayar ta kwanta. Washe gari kuwa tana gama abinda zatai ta kule a daki. Mami ce ta shigo ta ce, Dady na neman ta. Wata faduwar gaba ta ji. Haka ta mike ta dauki mayafin rigar dake jikin ta ta nufi falon Dady A hanya ta hadu da Yaa Aslam shima zai je dakin. Kallon sa tayi ta dauke kai sannan ta durkusa ta gaishe shi. Amsawa yayi yana binta da wani kallo mai cike da tsantar kauna. Kai ta kawar tai saurin shigewa dakin Dady Bayan ta yabi yana murmushi wanda shi kadai yasan ma'anar sa. Asma'u na shiga tayi gefen Dady, gaishe shi tayi sannan ta kalli Yaa Buhari dake dakin shima ta gaishe shi. Mami ce ta shigo ta zauna. Gyaran murya Dady yayi sannan ya ce, "Ayi salati ga Annabi (SAW)." Bayan anyi akai addu'a ga wanda da suka riga mu gidan gaskiya sannan. Ya kalli Asma'u ya ce, " *Husnah* ba komai ne ya tara mu anan gun ba sai wani abun da nake son na sanar dake, abin nan kowa ya sani ke kadai ce kawai baki sani ba." Shiru yayi yana kallon Asma'u wacce duk ta gama tsorata bata san me zai faru ba. Dady ya ce, "Kafin nan ina son na tambaye ki shin *Husnah* kina da wanda kike so ne?" Faduwar gaban ta ce ta tsanan ta, wani gumi ya karyo mata. A gaskiya tana jin kunyar Dady dan ji take baza ta iya ce masa akwai wanda take so ba. Shiru tayi Dady ya kuma tambayar ta tayi shiru sai da ya tambaye ta sau uku bata bashi amsa ba sanna ya ce, "Wannan ya nuna min baki da wanda kike so kenan." Da sauri ta dago kai ta kalli Dady sai kuma ta kalli Yaa Aslam da ya zuba mata ido. Kasa tayi da kanta. Murmushi Dady yayi ya ce, "To Alhamdulilah! Akwai wani alkawari da na dauka tin kina shekara shida. Ba wani alkawari bane sai na bawa Aslam auren ki," Da sauri Asma'u ta dago tana kallon Ya Aslam. Murmushi ya sakar mata ya kanne mata ido daya. Dady ya ce "Aslam shi ya hana a fada miki ya ce, sai ya nemi soyayar ki gashi kuma ba tambaye ki ba Wanda kike so kinyi shiru." Fuska Amsa'u ta rufe da tafin hannu. Dady ya kalli Aslam ya ce, 'To kai har yanzu baka nemo soyayyar taka ba dan haka ka sake zage dantse." Dariya dakin sukai gaba daya. Dady ne ya kara yin gyaran murya ya ce, "To yanzu Aslam yazo akan batun auren ku. Ya ce, so yake da kinga gama karatu ayi komai a gama, dan haka na kira ki na shaida miki an bada ke ga Dan uwan ki Aslam." Kai tayi kasa dashi tana jin wani sanyi kamar zai me murnar ta taki ta rufu. Kamar yadda Aslam ma bakin sa ya kasa rufuwa. Dady ya ce "dan haka muna addu'a Allah ya tabbatar da alherin sa a cikin wannan al amarin." Dakin gaba daya suka amsa da "Ameen!" Dady ya ce, "Yau nafi kowa farin ciki da na sauke wannan nauyin a kai na da kaina. Allah yasa Asma'u ta zama matar ka ta sunna." Suka kara amsawa da "Ameen!" Dady ya ce, "Zan fi kowa farin ciki ko a yau na mutu nasan *Husnah* ba zatai maraici mai yawa ba dan na tabbata Aslam da Buhari zasu kula dake iya kar iya yawar su. Ina fatan *Husnah* ki zama mace ta gari ga mijin ki. Aslam yana son ki so tsakani da Allah nasan duk wanda zai zo ya so ki bai zai kai kamar yadda Aslam ke son ki ba. To Alhamdulilah kema kina son nasa naji dadi. Allah yai muku albarma." "Ameen!" duk suka amsa Dady ya ce, "Shikenan kuje daman kiran kenan." Asma'u ce ta mike ta fice duk kunya ta kamata. Dariya Dady yayi ya ce, " *Husnah* kenan." Mikewa Aslam yayi shima yayi dakin sa. Waya ya bugawa Dadyn sa yana cewa ya shirya, auren sa ya kusa fa. Dariya yabawa Dadyn sa Dadyn sa ya ce "Allah tabbatar da alheri," "Ameen!" Ya amsa Tin lokacin Asma'u ta kasa fitowa falo sai bayan la'asar da taji gidan shiru shine ta mike ta shiga wanka. Fitowa tayi ta shirya cikin bakin dogon siket sai wata riga mai dogon hannu Ash kala wacce akai mata ado da bakaken stone. Hula kawai ta saka ta fita daga dakin. Mami ta gani zaune a falo. gefen ta ta zauna ta ce, "Mami sannu da gida" "Yauwah!" Mami ta amsa. ta mike ta fice. Garden ta nufa ta zauna a inda suka saba zama ita da Yaa Aslam. Ido ta lumshe kamar me bacci ta tafi can duniyar tunani. Aslam kuwa tin da ya dawo daga massalaci ya nufi garden din shima. Da farko zama yayi sai da yaga ba kowa sannan ya mike yana zagaye garden din. Iska mai dadi tare lumlume na ratsa sa. Yanzu haka gajiya yayi, ya juyo ya dawo dan ya zauna. Kamar a mafarki ya hangonta kwance ta lumshe idon ta. Wani dadi yaji ya lulube shi. A hankali ya karaso inda take. Zama yayi a kujerar dake gefen ta sannan ya hura mata iska a kunnen ta. Ido ta bude da sauri Yaa Aslam ta gani zaune a gefen ta sai murmushi yake sakar mata. Mikewa tayi zaune ta kasa dauke idon ta daga kallon sa. Murmushi yayi ya hure mata idanun ta da iskar bakin sa. Murmushi tayi ta dauke kanta daga kallon sa cikin jin kunyar sa. Ya ce, "Baby ya kamata muje naga asibitin ki," "To muje." Ta fada tana mikewa. Kamo hannu ta yayi ya ce, "Ina kuma zaki?" "Mami zan fadawa." Sakar ta yayi ya ce, "Ina jiran ki a mota." Cikin gida ta shiga ta dauki after dress sannanta sanar da Mami inda zasu. Adawo lafiya Mami tai musu suka fita. A hanya ba wanda yace da dan uwan sa kala. Ita Asma'u sai yanzu take jin kunyar Yaa Aslam dan yanzun ta tabbatar da gaske dai shi zata aura. Shi kuma ya rasa me ya hanashi jan ta da hira sai da lokaci kadan kadan ya kalle ta ko ya kamo hannun ta ya murza. Da haka har suka karasa asibitin. Katon Asibiti wanda Dady yasa akai mata ginin zamani mai kyau. Komai na cikin asibiti mai kyau da tsada ne. Har office din ta sai da suka shiga. Ya Aslam sai yaba wajen yake. Duk da nashi asibitin yafi nata girma amman tsarin nata ya burge shi sosai. Sai da suka gama kalla ya ce, "Baby na kince dai in munyi aure yau muna kano gobe muna Abuja ko?" Kallon sa tayi dan bata gane maganar tasa ba. Ya ce, "Eh man ai dole muna zuwa duba asibitin mu ko?" Murmushi tayi ta daga masa kai, Gida suka koma ana kiran sallah magariba. Asma'u ce kawai ta shiga ciki shi kuma ya tafi massalaci. *Muje zuwa* *INDABAWA* [1/18, 14:20] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* *Gidan Amanci da albarka* Dedicated to *My Lovelly Momy* *121-125* An Ruwaito Daga *Abdullahi bn Mas'ud (ra)* Ya Kasance Idan Ya Samu Labarin Fitowar Rana Yana Cewa:_ *{ﺍﻟْﺤَﻤْﺪُ ﻟِﻠَّﻪِ ﺍﻟَّﺬِﻱ ﻭَﻫَﺐَ ﻟَﻨَﺎ ﻫَﺬَﺍ ﺍﻟْﻴَﻮْﻡَ ، ﻭَﺃَﻗَﺎﻟَﻨﺎ ﻓِﻴﻪِ ﻋَﺜَﺮَﺍﺗِﻨَﺎ}* _*"Alhamdulillahil Lazi Wahaba Lanã Hazal Yauma Wa Aqãlanã Min Atharãtinã²".*_ Yana dawo daga massalaci ya kira ta awaya kan ta same shi a garden. Mikewa tayi ta fita ta kofar kitchen ta shiga yana zaune akan kujera ta karasa gun sa. Zama tayi ba tare da ta ce kala ba. Kallon ta yayi yai murmushi ya ce, "Baby na ya kika ji batun Dady dazu." Murmushi tayi ta ce, "Me Dadyn ya ce?" Murmushi yayi ya ce, "Wallahi baza ki kunna ni ba. Kinji komai da ya fada yanzu kin kara tabbatar da irin son da nake miki." Kai ta gyada ta ce, "Daman can na yadda da son da kake min." Murmushi yayi ya ce, "Alhamdulilah nagodewa Allah Zuciya ta ke kadai takewa na amince ki rike ta har abada." "Ya Aslam kenan!" ta fada. Yace, "Eh! Man kada ki taba zaton zan yaudare ki" Tace, "Nasan baza ka taba bama." Yace, "Yauwah Love." Sukai murmushi a tare, Asma'u ta ce, "Nima Zuciya ta kai kadai take yabawa dan tasan ka riketa ba da yaudara ba." "Da gaske." "Eh!" Ta fada tana dage masa gira. ya ce, "So hadi na Allah ne Asma'u, Zuciyata ke kadai ta nuna min. Na riga na sanarwa da Momy da Dady da Dady da Mami, da duk wanda muke mu'amala dasu in babu ke sai dai na rasa rayuwa ta." Ido ta zaro, "Su Momy," Yace, "Eh! Mana ai kowa yasan son da nake miki in aka raba mu zan iya rasa rayuwa ta." Murmushi tayi ta ce, "Allah ma ya kiyaye." Ya ce, "Ameen!" Tace, "Tin da Dady ya bayyana, min son ka akan kai ne, mijina baka ji yadda naji ba. Saboda Allah yasa ga wanda nake so aka hada kaga yafi dadi ko." Ya ce, "Shiyasa nacewa Dady kar a fada miki sai na kama bakin zaren!" Murmushi tayi, ta ce, "Wane zaren kuma" Ido ya kashe mata. "Zuciyar ki man. Hmmm *Husnah* baki san yadda na riki soyayyar ki a raina ba. Ta zama abin yi dare da rana. Soyayyar daraja ne da ita. Samun irin taki shine burin ko wane me hankali. Bana son na taba yin nesa dake. Kin shiga zuciya kinyo kafuwa. Ni dake babu rabuwa koman dadewa." Kallon sa ta tsaya yi. "Kai ma kasan kaine zabin rai na. Zuciya ta, ta adana soyayyar ka ba wanda ze maye gurbin ta. Sa'a ni na sama tinda na samu gwarzon masoyi kamar ka. Kai ka ke sani addu'ar neman miji na gari, kuma nasan Allah ya amsa min da ya aikon da kai a matsayin masoyi wanda nake fatan shine miji na." "Gaskiya ne. Dace da masoyi shine ribar soyayya. Nasan sabon da mukayi ni dake sai dai a kira mu tagwaye, ko yaushe in na tina ki nakanyi murmushi da jin farin ciki a cikin zuciya ta." Murmushi tayi, ta sauke ajiyar zuciya me karfin. Ya ce, "Lafiya?" Ta ce, "Ya Aslam in na tuna da rabuwa ne sai naji zuciya ta tayi min rauni" Kallon ta yayi ya ce, "Haba *Husnah ba mun kashe wannan maganar ba ne." Kai ta gyada masa ta ce, "Eh!" Ya danyi murmushi shima. Ya ce, "To Bazamu rabu ba sai dai mutuwa itama insha Allahu tare zata dauke mu." Kai ta langwabar tace, "Allah yasa!" Ya amsa da "Ameen." Dan shiri sukai sai kuma yace, "Yauwah kinga tin yanzu sai mu fara tsara yadda bikin mu zai kasance ko?" Murmushi Asma'u tayi tace, "Kai Yaa Aslam tin yanzuu." Yace, "Eh man. please My love, let's talk about ourselves, our future My dear, sbd managers sun ce, he who failed to plan he plan to fail." Kallon ta ya yi sannan ya cigaba da cewa, 'My love, ni yanxu bani da wata agenda da ta wuce naga mun gina rayuwa me kyau ni da ke my dear. My yanxu misali nan da yaushe ya kamata ace mun fara shirin auren my?" Asma'u ta dan ja numfashi ta ce, "Ni ban sani ba." Dariya yayi ya ce, "Toh Ashe kuwa abin xai xo muga bamu tanadi komai ba my. Indai haka xakina cewa my." Asma'u tayi murmushi ta yi kasa da kai ta ce, "Haba To ni me zance?" Dariya Aslam ya karayi ya ce, "ke kuwa kike da abinda xaki ce, My just ra'ayin ki xaki fada da abinda kike ganin ya dace musa acikin tsari Wanda may be ni hankali Na be kawo kai ba." Asma'u ta ce, "kamar me?" Ya ce, "Kamar ace a ra'ayin ki, May be akwai wani event da kike ganin kina bukata ayi." Kan Asma'u a kasa ta ce, "fadin ra'ayin ka naji." Ya ce, "My ina so if possible ace ran Friday xa'a daura mana aure after mosque." Murmushi Asma'u tayi dan itama tana sha'awar daurin auren ranar juma'a. Kai ta daga ta ce, "Yayi kyau nima ina son haka." "Yauwah koke fa. Sai batun sauran event me da me kike ganin za'ayi." Dariya tayi ta ce, "Duk yadda My yake so haka za'ayi." Numfashi yaja ya ce, "Kinsan sauran Event duk naku ne, daurin aure da dinner sune kadai namu." "To ni dai nasan Mami zata yi yini da kamu daga haka bansan me kuma ba." Murmushi yayi ya ce, "Shigar da zamuyi kuma fa?" "Wayoo Ya Aslam ni bansan yadda za ayi ba." Ta fada yana turo baki. Aslam ya yi dariya ya ce, "Wallahi *Husnah* zamu bata, sai kace bakya son maganar auren tamu. Oya fada min wane kalar dressing kike so muyi ran dinner." Baki ta turo tana kun kuni. Dariya yayi ya ce, "Eh sai kin fada. Kaji yarinya daga an mata maganar aure ta maidani sirikin ta. Maza fada min ko na fadawa Dady ayi auren ending month din nan." Dariya tayi ta ce, "Ayi man." "Haka kika ce?" Kai ta girgiza ta ce, "A'ah!" Ya ce, "To fada min." Shiru tayi sannan ta dago ta ce, "Ran Dinner ina son dressing din gloding kala. Ran Daurin aure kuma farar shadda zaka sa ko blue?" Kallon ta yayi ya ce, "Ke nake son ki zabar min. Amman gani nake fara zata fi saboda ranar farin ciki ce kamar yadda zuciya ta take fara haka nake komai nawa ya zama fari." Murmushi tayi ta ce, "To kaga ka zabi abin ka." "Haka ne, sai na ranar yini." Dariya tayi ta ce, "Duk kalar da ka zaba." "Ok ranar zan saka blue din shadda dan haka kema ki saka something da zai hau dashi." Kai ta daga ya ce, "Gobe zan sa Momy ta tanadar mana kayan." Kallon sa tayi tana dariya. Ta ce, "Ya Aslam duk saurin nan fa." "Kedai bari wallahi ji nake kamar na matso da kwanan nan kusa " Dariya tayi ta ce, "In kana wannan zumudin sai ina jin tsoro kar wani abu ya faru." "Kefa haka kike. Dan Allah ki daina sa haka a ranki za'ayi komai lafiya a gama lafiya da izinin mazon Allah (SAW)" "Allah yasa to!" "Ameen!" Kallon ta yayi yai.murmushi. "Lafiya?" Ta tambaye shi. Murmushi ya karayi ya ce, "Wai ya zanji ranar da My ta zama mallaki na." Kasa tayi da kai. Ya ce, " *Husnah* duk ranar da kika zama tawa wato mallaki na sai nayi azumi guda bakwai na godiya ga Allah da ya mallaka min ke." Dariya tayi. Ya ce, "Ranar zan yi abinda ban taba sanin me zan yi ba har yanzu amman ranar zata zama rana mafi soyuwa a rayuwa ta." "Yaa Aslam kenan!" Murmushi yayi ya girgiza kai ya ce, " *Husnah* kenan amman dai baza kizo kina min kuka ba ko? Tinda gaki a gun life partner din ki." Murmushi kawai tayi. Aslam ya ce, "Wannan murmushin naki make me go crazy." "Allah ko Yaa Aslam kana kashen bakin magana ne." Murmushi yayi ya ce, "Plz don't u ever forget I love u. (Dan Allah kada ki taba mantawa ina son ki.) Plz promise to never leave me even if there are thousand and one reason to. (Dan Allah ki min alkawarin baza ki taba bari na ba ko da akwai dubun nan dalilai da huja da zaki) Plz promise to stay with me no matter how hard or difficult the relationship might be. (Dan Allah kimin alkawarin zaki kasance dani duk rintsin yanayin da zamu tsinci kan mu a ciki.) Do u konw why am saying all this? (kinsan saboda me nake fadan duk wannan) Because I never ever want to loose u My, If I loose u, I have lost a grate part of me (saboda bana son na taba rasa kine tawan, in na rasa ki na rasa wani babban bangare daga gareni.) Idan na rasa ki Nayi mummuna rashi My To me u are the perfect wife and I just want to make u mine. (A waje na, ke ce cikakiyar mata. Kuma kawai ina son na mai dake tawa.)" Kasa tayi da kanta. Mikewa yayi ya dawo gaban ta. Kan ta ya dago idon ta a lumshe. "Dan Allah ki amshi alkawari na." Dagowa tayi ta ce, "Yaa Aslam komai naka ina son ya kasance gaskiya dan nima shine duk burika na. Ina addu'a Allah yasa duk abinda ka ambata ya zama gaskiya da nafi ko wacce mace farin ciki da samun soyayar gaskiya." "Nagode *Husnah* Nagode Allah mallaka min ke." "Ameen!" Ta amsa. Mikewa tayi ta ce, "Mu shiga ciki ko?" Kai ya gyada mata yabi bayan ta. *INDABAWA* [1/18, 14:20] Maryam S Indabawa🥰:  *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* *Gidan Amanci da albarka* Dedicated to *My Lovelly Momy* *126-130* An Kar6o Daga *Abi-Hurairah (ra)* Yace: “ *Manzon Allah(ﷺ)* Ya Hana Mutum Riqe Kwankwasonsa a Cikin Sallah”. *(Bukhari da Muslim)* a Lafazin Muslim: *“Shine Mmutum Ya Sanya Hannunsa a Qugunsa”.*_ Satin Yaa Aslam daya ya juya da shirye shiryen bikin su. Dan yana komawa yasa Momy a gaba dole suje dubai su hadu kayan lefe. Momy ta ce, ya bari lokaci ya kara karatowa. 'Ki yayi ya ce shidai su tafi. A satin da ya dawo a satin suka tafi hado lefe. Siyayya mai yawa da tsada sukayo. Duk abinda yaga ya burge shi ya ce a dauka. Haka nan Momy itama da ta iya zabe kaya masu kyau da tsada ta dinga siya. Kaya sai da suka hada set akwati uku amma basu isa ba. Sosai Momy ta hado mata kayan kwalliya da english wears dan ta san irin shigar da Asma'u take kuma tasan Asma'u yar gayu ce. Haka suka dawo gida da niki nikin kaya. Shi Dady da ya gani ma cewa yayi sunyi kadan. Kudi ya bayar a dado kayan da gwala gwalai. Har da Mota Dady ya ce a hada mata. Momy tace, "Dady ai ba yanzu za akai kayan ba." Dady ya ce, "Me za'a jira to. Kunga akai kaya ai sa rana kawai komai yazo daga baya." Momy ta ce, "To Dady in haka ne, ai kune masu kai kayan dan na fison maza suyi komai. Mu masha biki daga baya." Dady ya ce, "Zan fadawa su Alhaji Aliyu da Ahaji Abubakar da Dadyn Asma'un ma. Amman ni ban ga amfanin ajiye laifen ba akai musu kawai a huta." Kai Mami ta gyada ita ma dai gara akai musun kawai. Amman kuma abu kusan shekara guda. A cikin satin akai wa su Dady magana kan za a kawo kaya. Dady cewa yayi baiyi wuri ba tinda abinda saura. Amman Dadyn Aslam ya ce gara a kawo ai kamar yau ne. Rana suka saka aka kai komai da komai. Aka sa ranar auren su nan da shekara daya. Sai kayan lefe da aka kai. Kayan sosai Mami tayi fada wai sun zubo kaya da yawa. Momy ta ce, to in bata kashewa Asma'u kudi ba wa zata kashe wa. Ta ce, "Amina kada ki manta fa haka kawai ma kaya nake siyawa Asma'u bare kuma yanzu. Ki daina nuna min ke kika haifi Asma'u to wallahi ji nake kamar ni na haife ta. Kinsan dai uwa daya uba daya ba wasa bane." Mami ta ce, "Haka ne Yaya amman kun kashe kudi da yawa." Momy ta ce, "Akwai kayan fitar bikin su ma da za a aiko dan haka ki zuba idon zuwan su. Suna gun dinki na bada a dinka mata su." "To Yaya angode Allah kara girma." "Ameen! Zancen kayan kitchen kuma na gama da komai." Haka suka gama wayar Mami na kara duba kayan da aka kawo. Asma'u kuwa duk ji take kamar a mafarki wai kayan lefen ta ne. Ji take kamar wasa kamar ba zata auri Yaa Aslam ba. Tinda aka kawo kayan ta sanar da Zainab. Zainab kuwa ranar da ta sanar mata tazo ganin kaya. Sai zolayar ta take. Asma'u dai sai dai tayi murmushi. Bakin ta ya mutu sai dai dariya ko murmushi. A kwana kin nan wata shakuwa ce ta kara shiga tsakanin Asma'u da Dady. Dan yanzu wani lokacin baya zuwa office ko da yaushe tana tare da shi. Kullum maganar sa daya ce " *Husnah* ki rike Aslam. Aslam masoyin kine, bani da burin da ya wuce naga auren ku. To in Allah ya nuna min zanyi murna. Haka nan in Allah bai nuna min ba shima zanyi murna dan nasan na bar ki a hannun wanda zai kula dake ko ba aure a tsakanin ku." Yayi shiru sunan ta ya kira ya ce, " *Asma'u* " Da sauri ta dago kanta. dan Dady baya kiran ta da Asma'u. Murmushi ya sakar mata, ya ce, " *Husnah* ki kasance mace ta gari a wajen mijin ki. Kiyi koyi da halin Mahaifiyar ki. Ni Nasan wace, *Husnah* to ina fatan halin da nasan ta da shiki koyi dashi." Dady a ko da yaushe bai da maganar sai akan ta rike Aslam. Aslam masoyin ta ne. Sai kuma nasiha da kullum suka zauna zai na mata kan ta.kula da mijin ta tai masa ladabi da biyayya. In ko ba haka ba sai ya ce, " *Husnah* ko na mutu ina son ki kasance cikin min addu'a sannan ki sawa ya'yan ki sona da min addu'a in Allah yayi ba xan ga lokacin ba. Ki kula da ya'yan ki. Ki basu tarbiyya mai kyau. Allah miki Albarka Allah yasa ki a gidan Aljanna Allah ya miki albarka." Kullum sai ya nanata mata wanda nan kalaman kullum. Wani lokacin tare ya shirya musu tafiya suka je dan siyan kayan dakin ta. In ta nuna abu ya ce, a bata irin sa wanda yafi shi tsada. Kaya masu tsada da kyau ya siya mata. Kaya sosai ya lodo aka kawo gida. Daki uku aka dure kayan. Da Asma'u ta ce, "Dady kamar an siyo kayan nan da wuri" Sai ya ce, " *Husnah* gara na siya tin yanzu ban sani ba ko zan kai lokacin ko bazan kai ba. In na kai Alhamdulilah ga kaya nan sai dai nagan su kamar a sama. in kuwa ban kai ba kinga Mamin ki ta huta sai dai a dauka kawai akai. *Husnah* bana son na mutu da nauyin ku ta wani abu ban muku ba. Na baku ilimi daga arabi har boko to ba abinda zance da Allah sai godiya ko a yau na mutu naci riba dan na ilimantar da ku. Bayan nan na baku tarbiyya wacce kowa yake sha'awar ku ta wannan tarbiyyar taku. To nikan me zance da Allah sai godiya da ya bani ikon daura ku akan dai dai. Gashi duk cikin ku na baku abinda zaku rike kan ku da mahaifiyar ku ko bani da rai. Asibitin can naki ne halak malak dan na rubuta a takardun suma. Kamfani na na sharada kuma na bawa Buhari. Wadan can gidajen na kwandila na barwa Mamin ku. Ina fatan ko bayan raina kar ku shiga cikin kuncin rayuwa. Alhamdulilah da Allah ya nuna min wannan lokacin lokaci daya nake fatan Allah nuna min shine. Allah ya nunan ranar auren ki. Kasa tayi da kan ta ta amsa da Ameen.Kalaman Dady ba karamin kashe mata jiki suke ba. A asibiti kuwa Sosai take da kokari dan duk abinda aka daura ta akai tana yin sa bakin kokari. Ga Yaa Aslam dake kara koya mata. Sir Sabir kuwa yana yawan zuwa ya gaida Mami ya tafi duk da duk zuwan da zai yi baya samun Asma'u a gida. To shima yanzu ya bar Makaranta ya koma asibiti. Son Asma'u sai daduwa yake a cikin zuciyar sa. Sako kuwa kullum sai ya tura mata amman sam ko reply. Hoton ta shi kadai yake kalla yaji dadi a zuciyar sa. Amman kullun da ita yake tashi da ita kuma yake kwanciyya. Haka yau kamar kullum bayan ya koma gida yai wanka ya shirya cikin wani tissue yadi fari. Ba karamin kyau yai masa ba. Fitowa yayi yaiwa Mamah sallama ya fita. Kai tsaye gidan su Asma'u ya tafi. Bai da buri da ya wuce yaga Asma'u. Asma'u tana gida yau dan ta yi targade a garin hawa sama yau duk gidan sun san Asma'u taji ciwo. Tana jikin Mami sai raki take mata. "Uhm wayoo Mami kafa ta." Mami kuwa sai lallashin take tana mata sannu. Duk ta rasa inda zata saka 'yar tata. Dady ya kira shima yana tambayar kafar Asma'u, Wayar Mami ta bata yai mata sannu sannan ya ce, me take so? Fada masa tai. Sukai sallama, tana cikin yiwa Mami shagwaba akai yo sallama kan Mami tayi bako. Izinin shigowa Mami ta bayar. Tana kwance akan kafar Mami tana tsiyayar da hawaye ya shigo. Da Sallama ya shigo Mami ce ta amsa masa ya shigo ya zauna. Asma'u dake cinyar Mami tayi juyi ta gyara kwanciyya ta ce, "Mami kafa ta." Shigowa yayi. Mami ta ce, "A'a Sabir ne?" "Eh wallahi Mami." Ya zauna suka gaisa, Asma'u ce ta kara juyi ta bude idon ta. Sabir ta gani da sauri ta mike zaune tana daura kan ta a kafadar Mami. "Ina yini?" Ta fada tana kamo hannun Mami. Amsawa yayi ya ce, "Yau bakije asibitin ba." Mami ta kalla. Mami ta ce, "Wai nan targade tayi shine fa take ta kuka ka ganta nan sai kace ba mace ba." Baki Asma'u ta turo, Sabir kuwa Murmushi yayi ya ce, "An duba kafar?" Kai Asma'u ta daga. Ya ce, "Zo naga kafar." Kamar baza taje ba ta mike ta karasa inda yake da kyar take tafiya. Kafar ya duba ya dan taba ta saki kara tana rike hannun sa. Lumshe ido yayi jin hannun ta mai laushi da ya ji da ta haifar masa da kasala. Da kyar ya ce, "Mami gyaran ne bai ba shiyasa." Mami ta ce, "Haba nifa ince tin dazu sai kukan kafar take." Kafar ya kama ya ce, "Mami kuna da man zafi." Eh Mami ta fada ta hau sama, kallon ta Sabir yayi. Kanta a kasa ta kasa dagowa ta kalli fuskar sa. Shi kuwa kallon ta yake kamar ya samu TV sai da yaga kamar zata dago sannan ya dauke kan sa. Mami ce ta sauko rike da man zafi a hannu ta mika mata. Amsa yayi yai tofi ya daura hannun sa a kan kafar ya danna ya ja. Ihu ta saki tana kiran Mami. Kara tayi tai saurin rike hannu. Hannun sa ya zare daga nata, ya karayin tofin yana jan kafar. Kuka sosai Asma'u take, Sai da ya tabbatar da kafar ta gyaru sannan ya bar ta. Akan kafet din falon ta kwanta tana kuka, hannun ta rike da kanta. Mami ce ta mike ta kawo Sabir lemo da ruwa, sannan ta tahowa da Asma'u ruwa. Kama Asma'u tayi ta kai ta kan kujera, ruwan ta sha, sannan ta langwabe a jikin Mami sai bacci. Sai magariba sannan Sabir ya tafi. *INDABAWA* [1/18, 14:21] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* *Gidan Amanci da albarka* Dedicated to *My Lovelly Momy* *131-135* Asma'u kuwa sai Magariba ta tashi. Tana tashi taji kafar ta saki. Mikewa tayi ta haye sama tai alwala tai sallah. Tana idarwa Yaa Aslam ya kira ta. Kafar ya tambaye ta ta ce, "Ai Yaa Aslam sai da aka kara gyara min ashe bai gyaru ba." "Ayyah sorry my dear da zafi ko. Sorry." "Yaa Aslam ai zafi har ba'a magana." "Sannu toh!" Daga haka suka cigaba da hirar su. Yau takanas Maimuna ta wanko.kafa tazo gun Asma'u. Dawowar Asma'u kenan daga Asibiti aka zo akace ta yi bakuwa. Sakowa tayi. Wa zata gani in ba Maimuna ba. Cikin shigar ta, ta riga da zani sai hijab din ta iya gwiwa. Asma'u da murna ta karasa wajen ta ce, "Lallai yau Maimuna ce a gidan namu." Maimuna tai murmushi ta ce, "To ina kewar ki ba dole na zo mu gaisa ba." Gaisawa sukai sannan Asma'u ta kawo musu abinci suka ci suka koshi. Wajen Mami ta kai ta suka gaisa sannan tace tafiya zatayi. Dubu biyar Mami ta bata tana mata godiyar ziyar da ta kawo musu. Har waje ta rakata dan sai da ta hau Napep sannan sukai sallama ta juya gida. Wata mota ta gani wacce kwanan nan kusan kullum sai ta ganta a layin ta rasa motar wace, ga bakin glass da take dashi. Motar ta kuma kalla ta shige gida abinta. Sabir dake cikin motar ya yi murmushi ganin ta kallon da ta tsaya yiwa motar. Ya tabbata ta fara gane da zaman motar a wajen. Motar ya tayar ya bar unguwar ransa fari tas yaga abinda yake son gani. Kwanci tashi ba wuya a wajen Allah. Yau gashi sauran wata uku su Asma'u su kammala karatun su. Yau ma kamar ko da yaushe da yake asabar ce suna zaune, a falo ita da Dady Dady ne ya kalle ta ya ce, " *Husnah* ba abinda kike bukata a kara siya miki." Kallon Dady tayi ta ce, "Dady da sauran lokaci fa." "Haka ne, amman na fison komai na gama shi da wuri dan bamu san me lokaci zai bayar ba " "Haka ne Dady. Amman ni bana bukatar komai." "Kin tabbata?" "Eh Dady." "Shikenan na miki transfer din kudi ta account din ki kingan su." Kai ta girgiza ta ce, "A'ah!" "Ki duba wayar ki, zaki gani. Dan haka ki ajiye in lokacin bikin yazo in kina bukatar kudi ki huta ba sai kin hau tambayar Mami ko Yayun naki ba." Murmushi tayi ta ce, "In ban tambaye su ba ai ina da Dady ko?" "haka ne! Kina da Ni amman in ina nan ba." Murmushi tayi ta ce, "Dady tafiya zaka yi ne?" Kai ya girgiza ya ce, "Ko daya in na mutu nake nufi." Damuwa ce ta sauka akan fuskar Asma'u sosai har ta kasa furta komai. Dady ya ce, "Haba *Husnahn Dady* mene na bata rai dan na fadi abunda dole ne ya faru. Ki daina sa damuwa aranki nasan ko na mutu kina da masu rike ki amana. Amman mutuwa tana kan kowa. Kowa lokaci yake jira da tazo kuma bata jira dauka kawai take. Gara duk abinda zamu nayi muna tunawa da ita. Kuma muna sawa a ran mu a ko da yaushe zaata iya zuwa ta dauke mu. Ki daina damuwa. Allah shi ya tsara mana rayuwar mu kuma in yai niyar mutun ya rayu sai kiga ya shekara nawa ma bai mutu ba. Ina iyayen mu duk sun mutu to muma haka wata rana zamu tafi. Fatan mu da addu'ar mu Allah yasa mu cika da imani kuma Allah yasa can ta fi nan." "Ameen!" Mami ta fada dan duk tana jin abinda suke fadi. Murmushi Asma'u tayi ta ce, "Mami kinga Dady yai ta kawo maganar mutuwa. Mami nifa bana son maganar mutuwan nan." Dariya Mami tayi ta ce, "Oh su Asma'u har yau ba a girma ba. To ya zamu Allah ya bamu gadon ta kowa sai ya mutu kuma tunawa da mutuwa yana daura mu akan hanyar Allah yadda zamu gyara kura kuren mu. Ki daina damuwa dan Dady ya kawo magane mutuwa. Yana da kyau ana tinawa da ita." "To Mami Allah yasa mu gama da duniya lafiya. Allah ya mana makoma da gidan Aljanna in lokacin yayi." "Ameen *Husnah* dan Allah kar ki manta kina sa ya'yan ki suna min addu'a." "Insha Allahu. Dady ka daina sa wannan a ranka. Kai ma zaka rayu da su. Su sanka insha Allahu." Murmushi Dady kawai yayi, daga haka suka cigaba da taba hira. Aslam fa ba zama lafiya tinda abin nan ya kara karatowa ya kara burkice ya duk wani plan nashi na auren su ne. Bai da magana da shirye shirye in ba na auren su ba. Katon Gidan sa da ya gama dankarawa yasa akai masa fenti aka gyare shi. Lokaci kawai yake jira. Preety ce kwance akan kujera gefen ta kawar ta ce, Nene, kallon ta Nene tayi ta ce, "Haba Pretty ki hakura da yaron nan kina ganin ya kusa yai auren shi ma." Mikewa Pretty tayi ta ce, "Wallahi sai Aslam ya aure ni. Kinji na rantse ko zan yawo tsirara sai na aure Aslam. Ita kuma Asma'u take ko *Husnah* zata gamu dani sai ta dandani irin yadda naji da yake son ta ni baya so na." Ta fada tana girgiza kafa, Nene ta ce, "Pretty ki dai yi a hankali kinsan komai zakiyi akwai karshen sa ko?" Kallon ta Pretty tayi ta ce, "Ke dallah ya isa kuma daman ance makashin ka yana tare da kai. In ba haka ba duk yadda muke dake xaki ce na rabu da su ko me? To naki. Wallahi sai na samu Aslam ko da me zai faru daga baya." "Allah baki hakuri. Ban fada dan na bata miki rai ba." Tsaki Pretty tayi ta koma ta kwanta ranta a bace kamar me. Ita fa bata da buri da ya wuce ta ganta gata ga Aslam. Tana son Aslam ko dan gayun sa da iya shigar sa da kyan sa. Ba abinda ya yafi rudar ta kamar kyan sa. Ido ta lumshe tana murmushi ta ce, "Wa ya ga Pretty amaryar Aslam!" Ta bude ido ta yin shewa. Kallon ta Nene kawai tayi ta dauke kai. Asma'u ce kwance akan gadon ta tana amsa wayar Aslam. Sai murmushi take, ko magana ta kasa daga ta ce, 'Eh' sai kuma ta ce, 'A'ah' sun jima suna hira sanna sukai sallama. Kwanciyya ta gyara tana ayano gata ga Yaa Aslam anyi auren. Ido ta rufe da hannun ta alamar taji kunya. Can ta bude su, ta kurawa saman dakin ido. Tunanin yadda suka tashi tare da Yaa Asalm ta dinga yi har yanzu da suka girma har a kai maganar auren nasu. Murmushi tayi kafin ta ce, "Ni *Asma'u Husnah* in na rasa Yaa Aslam ya zanyi." Da sauri ta mike idon ta sun kawo ruwa ta ce, "Allah na tuba Allah kada ka jarabace ni da rasa Yaa Aslam. Allah ka bani Yaa Aslam." Ta koma ta kwana sai kuma kuka sai kace an dake ta. Sosai take kuka. bacci ne ya dauke ta shine aka samu tayi shiru. Tin lokacin jikin ta yai sanyi ta rasa me yake damun ta. Karfe sha dayan dare Bayan Mami da Dady sun tafi daki. Zama sukai Dady yana bata takardun kadarorin da ya mallaka musu. Mami ta ce, "Ai Dady da kabar su agunka." "A'ah ku rike abinku. Gara ki saba dan in bana nan yazai adana muku." Amsa Mami tayi ta ce, "Alhaji kenan." Yai mata murmushi. Alwala sukai suka kwanta. Can wajen karfe ukun Dare Dady ya farka da wani irin ciwon ciki. Ciwon ciki ne, wanda bai taba jin kamar sa ba duk da kwana biyun nan yana yin sa a dadafe a dadafe amman na yau ya banbanta. Tin yana daurewa har ya tada Mami daga Bacci. Mami na ganin sa a halin da yake ta mike da sauri tana tambayar sa, lafiya. Kasa magana yayi. Da sauri Mami ta mike ta kunna fitila. Ciki ta ganshi dafe dashi, maganin Ulcer, ta dauko ta bashi yasha. Dan lafawa yayi dan har ya fara bacci sai ya kuma tashi. Na wannan karan har yafi na dazu ganin wahalar da yake sha yasa Mami ta tafi dakin Buhari ta taso shi. Da sauri ya biyo bayan ta a durkushe su ka tadda shi ya dunkule gu daya sai juyi yake. Buhari ya ce, "Mami bari a fito da mota mu tafi asibiti kawai." Ya fita da sauri shi ya kama Dady, Mami kuma ta shiga dakin Asma'u. Zaune ta same ta akan sallaya, Asma'u na ganin Mami ta mike da sauri ta ce, "Mami lafiya?" Mami ta ce, "Dady ne ba lafiya." Da sauri Asma'u tayi waje. Mami ce tabi bayan ta. Mami ta ce, "Sunyi waje." Kasa ta nufa ta sauka daga benen. Tana zuwa har Buhari ya shigar dashi. Da sauri ta shiga mota ta zauna kusa da Dady. Tana rike hannun sa. Mami ce ta shiga ta zauna. Asma'u kuwa ganin halin da Dady ya shiga duk sai ta fita daga hayacin ta. Kuka take tana cewa, "Sannu Dady. Sannu" Duk bayan minti biyu sai ta kara ce masa sannu. Pls don't forget to press on start to vote. *INDABAWA* [1/18, 14:21] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* *Gidan Amanci da albarka* Dedicated to *My Lovelly Momy* *Momy nah a koda yaushe addu'a ta bazata taba karewa gareki ba.* *Kece komai nawa. Ina nufin komai fa.* *Masoya a ko da yaushe kune silar dariya ta. Bama in ina karanta comment din ku.* *To Alhamdulilah Da soyayyar ku a gareni. Allah ubangiji ya bar ni da ku.* *Gaskiya ina jin dadin yadda kuke bibiyar labarin nan.* *Masoyan Aslam* *Masoyan Sabir* Kuna ina ne? *136-140* An Kar6o Daga *Anas (ra)*, Lallai *Manzon Allah(ﷺ)* Yace: *“Idan Aka Gabato da Abincin Dare, to Ku Fara Dashi Kafin Ku Sallaci Magariba”*. (Bukhari da Muslim)_ Suna zuwa asibiti aka amshe shi. Sun jima akan sa dan har akai sallar asuba. Sallah Asma'u tayi ta jima tana wa Dady Addu'ar Allah ya bashi lafiya. Dady kuwa ganin jikin sa sai wasiya yake bayar wa yana cewa, "A kira masa *Husnah* ku kira min matata da 'da na da Auta tah *Husnah* " Da sauri Dr ya karasa ya kira su. Asma'u na shiga da gudu ta karasa wajen Dady ta rike hannun Dady tana jijigawa tana cewa "Dady gani. Dady ga *Husnah* ka." Dady dake kwance yana fitar da numfashi sama sama, ya kalli Mami da Buhari. Ya ce "Amina Allah miki albarka. Allah ya baki aljanna madauka. Buhari kai ma Allah maka albarka Allah ya saka a gidan aljanna Allah baka mace ta gari." Ya karasa maganar da kyar. Cikin sa ya kara rikewa ya kalli Asma'u ya sakar mata murmushi ya ce, "Ga *Asma'u Husnah* nan ku kula da ita. Ita ce, yarinyar karama kar ku bar ta tai kuka. Amina Allah miki Albarka. *Husnah* Allah ya miki albarka. Allah baki zuri'a ta gari Allah ya saki a Aljanna." Hannun Buhari ya kamo tare da na Mami. Kallon Asma'u yayi ya sakar mata murmushi. Kalamar shada ya dinga fadi a hankali. Mami ita take tayasa amsawa. Su Asma'u da Buhari kuwa gaba daya sun rikice da kuka. Can Dady ya saki hannun su idon sa ya lumshe, cikin firgice, Mami ta kwadawa Dr kira. Dr ne ya shigo ya duba shi. Kai ya girgiza kawai. Kallon sa Asma'u tayi ta ce, "Dr ya jikin nashi ne?" Kallon su Dr yayi ya ce, "Sai dai kuyi hakuri Allah ya amshi rayuwar sa." Asma'u dake tsaye wata juwa taji tana dibar ta. Daga nan duhu ya rufe mata idon ta. Zubewa tayi a kasa. Mami ma faduwar tayi. Buhari kuwa ya rasa ya za yi. Da sauri Nurse suka yi wani Daki aka kai Mami da Asma'u aka kwantar da ita. Suna kokarin ceto rayuwar su. Buhari kuma ya buga waya ya fadawa Uncle Abubakar kanin Dady da uncle ilyasu da kanwar sa. Sai Momyn Aslam da sauran yan uwa. Cikin minti kadan gida ya cika da jama'a. Mami da Asma'u kuwa suna Asibiti. Momyn Aslam a lokacin suka taho a jirgi. Karfe sha biyu aka sa za ayi jana'idar Daddy. Momyn Aslam na zuwa, ta zarce asibiti. tana zuwa Mami ta farka. Kuka Mami ta saka. Momy ta kama ta ta ce, "Haba Amina, me yasa zaki kuka ki sani kukan ki ba abinda zai karawa Abban Asma'u. Addu'a ce kadai zaki taya shi da ita Allah yai masa rahama.dan Allah ki daure kar ki bari ki saba da zubar masa da hawaye. Allahn da ya bamu shi yafi mu son shi dan haka hakuri zamuyi muna taya shi da addu'a." Sosai Momy tayiwa Mami nasiha mai ratsa jiki. Kukan ta daina amman fa zuciyar ta kamar zata fashe. Damuwa karara akan fuskar ta. Da haka suka mike suka yi gadon da Asma'u take. Tana kwance har lokacin bata san inda kanta yake ba. Momy ce ta zauna da ita aka tafi da Mami gida dan ganawa da gawar Dady. Aslam kuwa da suka taho Dadyn sa bai sanar da shi halin da Asma'u ke ciki ba. Dan haka duk yadda yaso ya ganta ya ga a halin da take ciki bai samu ba. Momyn sa ya kira ya ke tambayar ta ina Asma'u dan Allah ta fada masa halin da take ciki. Dan yasan a wannan lokacin Asma'u zata fi kowa jin mutuwar Dady. Duba da irin shakuwar dake tsakanin ta da shi. Komai in zatayi Dady ko abu zata yi tace Dady. Tafi yin shawara dashi akan da Mami. shiyasa yake son yasan a halin da take ciki. Haka ta ce masa tana asibiti in ta dawo zata duba masa halin da take ciki. Amman ya kwantar da hankalin sa tana lafiya. Suna cikin waya aka kawo Mami gida. Da sauri ya karasa gun Mami. Duk tausayin ta ya kama shi. Shi ya kamata suka shiga cikin dakin da aka kwantar da Dady. Addu'a Mami tai masa sosai, sannan aka zo aka dauki gawar ta shi. Duk yadda taso kar tayi kuka sai da hawaye ya zubo a idon ta. Kanwar Dady ita tazo ta shiga ciki da ita. Jama'a sun cika gidan makil da mutane. kowa sai mutuwar Dady yake ji, Dady mutumin kirki me kawaici da Hakuri da taimako. Dan haka kowa abin alherin sa yake fada da masa addu'a. Mami karfin hali kawai take domin tasan ta rasa farin cikin ta. Ta yi asara da baza ta taba maida kamar ta ba. Dan rashin Dady a garesu ba karamin gibi bane. Ana ta amsar gaisuwa Mami kuwa ta yi nisa cikin tunani, ga Asma'u, ba wanda tafi ji.kamar Asma'u. Asma'u kuwa da magariba ta farfado. Tana ta shi tasa kuka ina Dadyn ta. Sai kuma ta kuma fashe wa da Kuka ta ce, "Momy dan Allah ku kaini wajen Mami da Dady dan Allah Momy Dady bai mutu ba ko? Momy kada kice min ya mutu." Sai wani kukan Momy ma sai da tayi hawayen dan ba karamin tausaywa Asma'u tayi ba. Allura Dr ya karai mata ganin tana neman fita daga hayyacin ta. Sai da Dady yai kwana uku aka sallamo Asma'u, gida suka taho da Momy dake wajen ta in kaga Asma'u zaka ga ta rame sosai sai kace wacce ta dade tana jinya. Aslam da tare suke jinya a asibiti shima duk ya rame ya yi duhu. Tare suka dawo, Asma'u na zuwa gida tayi wajen Mami, ta rumgume ta tana wani kuka mai ban tausayi. Kuka sosai suka yi sannan Mami ta dago ta tana kallon ta. Ta rame har abin yai yawa. Buhari ya ce, "Mami ga Asma'u nan bata cin abinci ko tea taki amsa ta sha." Kai Mami ta girgiza ta jata jikin ta tana shafa bayan ta ahankali a hankali. Zainab da tinda akai mutuwar take zarya daga asibi zuwa gidan yau ma tana gidan. Dakin Asma'u suka shiga, Asma'u da ta kasa daina zubar hawaye daga idon ta. Abinci Yaa Buhari ya dauka ya kai mata ya ce taci amman sam taki ci. Yaa Asalm ya fadawa. Aslam da kansa ya shigo gidan ya shiga har dakin ta ya tadda ta kwance akan gado. Zama yayi a gefen ta ya dago ta. Tana ganin shine ta fada jikinsa tana sakin wani kuka mai ban tausayi. Rumgume ta yayi yana lalashin ta da kalamai masu nuni ga ban hakuri har tayi shiru sai ajiyar zuciya da take saukewa. A hankali ya dinga bata baki har ta yadda ya dinga bata abinci a baki. Ci take tana yamutsa fuska dan ba dadin sa take ji ba. Har wani daci yake mata a baki. Idon ta kuwa ya kasa tsayar da hawaye, a haka ta dan ci ta ce ta koshi. Tin daga lokacin kullum Asma'u na gefen Mami, dan ko bacci ta koma kullum tana gefen ta. Kullun kuwa Asma'u da zazzafi take kwana ta tashi. Amman da Mami ta ce zata bata da lafiya zata ce ta ji sauki. Ranar bakwai kuwa Asma'u kamar me kuka ta dinga yi dan har numfashin ta daukewa ya dinga yi. Yaa Aslam da Sir Sabir su suka tsaya akan ta. Da kyar suka samu numfashin ta ya dawo dai dai. Bayan bakwai kowa ya watse sai Momy da Aslam. Suma ana yin kwana goma Momy ta fara shirin tafiya. Hakuri sosai ta dinga bawa Mami. Sannan ta zaunar dasu gaba daya, ta kara basu hakuri sannan ta bawa Mami kudi masu yawa. Haka Momy ta tafi gidan ba dadi daga Buhari sai Aslam da Mami da Asma'u. Asma'u da ta zama shiru shiru ko magana batayi. In anyi abu sai dai ta kalli mutum ta dauke ido. Aslam kuwa kullum ya zauna sai ya san yadda zai sa tayi dariya. Aslam shike sa Asma'u yin hira ta dan sauko. In kuwa ba haka ba sai dai ta zauna tai ta zubar hawaye. Yau ma kamar kullum tana kwance akan gado, ba abinda take sai zubar hawaye tana tunanin Rayuwar su da Dady. Murmushi ta dan saki sai kuma, kuka da ya kwace mata. Aslam dake tsaye a kofar ya na kallon sanda tai murmushi sannan kuka yazo ya karaso gun ta da sauri. "Haba *Husnan Dady* yanzu haka zamu ta rayuwa kenan kullum kin ki ki sake, kina tunanin Dady zai ji dadi a halin da kike ciki. Haba *Husnah* a ko da yaushe Dady bai da magana da ya wuce yasan ko bayan ransa *Husnah* baza tai kuka ba saboda yasan damu. To menene amfanin namu da mu na nan zaki na kuka. Haba *Husnah* dady ba abinda yake nema gun ki sai addu'ar ki. Dan Allah ki daina wannan kuka. In ba haka ba ni bazan iya jurar ganin kukan ki ba zan tafi in hakan kike so." Hawayen ta, ta goge ta ce, "Na daina Wallahi Yaa Aslam na daina. Kar ka tafi ka barni." Murmushi Aslam yayi ita kuwa duk da hawayen da take yi gogewa wani ne yake kara daduwa. Jikin sa ya jata yana lallashin ta. *Hmmm kulli Nafsin xa'ikatul Maut.* *wannan haka yake* *Karki kuce saboda na sa Dady ya mutu. Haka rayuwa take, muma wata rana sai mutuwa.* *Hmmm kuyi hakuri haka tsarin littafin yake. In ba haka ba wani abu bazai faru ba. Nagode* *Nusaiba S Indabawa* Ki daure ki karanta littafin nan. Lol wai ita indai nayi littafi wani ya mutu bata karantawa saboda tausayi. *To sisto ki karanta dan nasan kina son karantawa. Mutu a kuma dole ce. Ke yanzu ina Dady, ya rasu. Sai dai muyi masa addu'a Allah ya kara masa rahama Ameen!* ALLAH KA JIKAN DUKKAN MUSULMAI. KA JIKAN YAN UWAN MU, DA KAKANNIN MU, DA IYAYEN MU DA YAYUN MU DA KANNEN MU DAMU KAN MU IN TAMU. TAZO AMEEN! *INDABAWA* [1/18, 14:21] Maryam S Indabawa🥰:  *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* *Gidan Amanci da albarka* Dedicated to *My Lovelly Momy* 141-145 An Kar6o Daga *Abi-Zarrin (ra)* Yace: *Manzon Allah(ﷺ)* Yace: *“Idan 'Dayanku Zai tsayar da Sallah Kada Ya Goge Kasa, Domin Rahama ce Take Fuskantarsa”.* (Mutane Biyar Suka Ruwaitoshi) da Sanadi Ingantacce._ Aslam yayi na mijin kokari wajen sauyawa Asma'u rayuwa. Dan kullum cikin daukar Asma'u ya kai ta wajen shakatawa ko ya kai ta shopping. Banda fina finen da yake siyo mata na ban dariya. Sai da yayi wajen wata biyu a kano sannan ya koma saboda wajen aikin sa. Duk da tafiyar sa duk wata kulawar da yake bata bai daina ba sai daduwa dda ta karayi. Sabir kuwa har Mamah ya kawo gida tai wa su Mami gaisuwa. Haka Maryam ma takanas ta zo kano dan Asma'u. Asma'u ma taji dadi. Haka nan Maimuna ma tazo tai mata ta'aziyya da yan department din su. Da kyar Asma'u ta koma asibiti, ta cigaba da rayuwar ta. Sabir ma yana zuwa akai akai yana duba su ya gaida Mami. Pretty ce zaune kamar an mata allura ta mike ta dauki ATM din ta da kudi ta zuba a jaka. Fita tayi ta tsaida mai Napep ta shiga. Tasha kai tsaye ta nufa. Tana zuwa ta hau motar Niger. Suna sauka Pretty ta tafi hotel. Sai da tai bacci ta huta tai wanka sannan ta ci abinci. Mikewa tayi sai kace wacce zata tashi sama. Fita tayi daga hotel din ta tsaida mai napep. Yana tsayawa ta fada masa inda zata sannan ta hau suka tafi. Yana tsayawa ta biyashi kudi sannan ta shige wajen. Waje ne kamar jeji haka ta kutsa kai. Sai da tayi tafiya mai nisa sannan ta karasa wajen Yar bukka ce, shi kuma yana zaune a gefen ta. Jikin sa ba komai sai ganye da yayi tufa da shi. Kalar fatar jikin mutumin baka kirin, haka nan jikin mutumin sai tashin wari yake. Idanun sa jajir kansa gashi ne yayi yawa dan sai a iya kitso ma akan shi. Yana zaune gefen sa tukwane ne. Tin da Pretty ta karasa wajen yake binta da wani fiti nan nen kallo. To kayan dake jikin ta ne kai ba zakai tunanin yar musulmi bace. Zama tayi nesa dashi dan ita ma tana kyamar sa. "Sannu boko na kan tudu." Ta fada tana kallon sa. Bakin sa ya bude wanda hakoran dake ciki sun zama ja dasu. "Kinji shiru ko?" Ya tambaye ta. Kai ta daga masa, murmushi yayi ya ce, "Eh kamar yadda na fada miki aikin yana da wahala ne," "Toh! Malam......" Tsawa ya daka mata. Ya ce, "Kar ki kara ce min Malam." "Dan Allah ka taimaka min wallahi zuciya ta zata iya bugawa in ban samu Aslam ba ka taimaka min." Kai ya daga ya ce, "Na fada miki aikin yana da wuta. Dan Aljannin da zai miki aikin ya ce, sai ya tara da ke tukkuna." Ido ta zaro ta ce, "Aljannin." Kai ya gyada mata. Ya ce "kar ki damu ki kwantar da hankalin ki. Ta jikina zai yi amfani dake," Ya fada yana lashe lebe. Kallon sa tayi a zabure ta nuna shi da yatsa, ta ce, "Kai!" Kai ya gyada ya ce, "Eh ni." Wani kallo ta watsa masa ta mike tabar wajen. Tana fita tayi gidan kawar ta wacce ta hada ta da bokan. Tana zuwa ta zube mata abin da ya faru, dariya kawar tata ta hau yi ta ce, "Amman wallahi har kin ban kunya, dan aljanni ya neme ki shine me?" "Ke dallah shine fa zai kusance ni. Haba kinsan fa ya yake, warin jikin sa ma kadai ya ishe ni." Pretty ta fada tana toshe hanci sai kace a gaban sa take. "Kinga ki ajiye duk wannan a gefe wallahi in har yayi abunda ya bukata ko to bukatar ki ta gama yi. Kin samu Aslam dan shi da wannan kwailar yarinya har abada dan nasan ko kallo baza ta ishe shi ba." Kallon ta Pretty tayi. Ta cigaba da magana. "Muma duk Boka yayi abinda kike tsoron yi dashi. Kuma ya kusan ce kinki zaki ji abinda baki taba ji ba. Kallon ta Preetty tayi a ranta tana son samun Aslam amman kuma tana kyamar ta yadda zata je wajen Boka. A haka kawar tai ta zuga ta har taji zata je dan biyan bukatar ta. Gida ta tafi tana tunanin taje ko kar taje. Wata zuciyar na cewa taje wata kuma tana hanata zuwa. A haka ta kwana da tunanin wata haryar da zata mallaki Aslam. Ganin bata da wata hanya yasa ta amince da zata koma gun sa. Mikewa tayi ta shiga wanka ta shirya cikin shigar banzar da ta saba yi. Abin hawa ta hau ya kai ta inda zata je. Ya dire ta tayi cikin jejin. Yana zaune kamar ko da yaushe, yana ganin ta ya saki fara'a. Karasawa tayi tana jin damuwar zuwan nata. Kallon ta yayi ya ce, "Ya kin amince ne?" Kai ta gyda masa dariya yayi ya ce, "To ai kin kyauta. Ki shiga daga cikin zan kira shi in zo zaki ganshi." Mikewa tayi tai ciki. Kallo ya bita dashi yana lashe leben sa. Can ya mike yayi cikin dakin da ta shiga yana wata irin tafiya. Sun dauki a kalla fin awa hudu zuwa biyar sannan Bokan ya fito yana gumi. Wajen zaman sa ya zauna. Can kuma sai ga pretty nan ta fito. Fuskar ta tai jajir da ita. Kallon malamin tayi ta bar wajen. Gida ta je ta dade tana dirje jikin ta sannan ta fito ta kwanta a kan gado. Ido ta lumshe tana cewa, Amman Malamin nan yayi. Dama ace Aslam ne. Ta yi juyi akan gado ta ce, "Asma'u kike ko Husnah ina tausaya miki duk randa na samu Aslam kin mutu." Cikin ta taji yana kukan yunwa ta mike ta fita gari dan samun abunda zata ci. Asma'u ce zaune a garden tana sanye da threequatern wando da riga karama a jikin ta. Sai hijab din ta da yake har kasa. ta rafka uban ta gumi. Ba wanda ta tino in ba Dady ba. Hawaye taji yana bin fuskar ta da sauri ta goge hawayen tina maganar Aslam da ya ce, " *Husnah* dan Allah kimin alkawarin ba zaki kara kukan akan Dady ba sai addu'a. wallahi kukan ki yana taba zuciya ta kamar yadda nasan ki cikin wani hali inda nima nake tsintar kai na a ciki. Ki daina kuka dan Allah ko bayan ido na kar kiyi kuka. In kuwa kikai kuka bazan taba yafewa kai na akan amanar ki da Dady ya bani ba." Murmushi ta dan saki na tunawa da Yaa Aslam. Tana da tabbacin Ya Aslam din ta zai rike ta amana dan tasan yana daga cikin masoyan ta na farko a duniya. Duk abinda yasan zai sa ta farin ciki shi yake buri shi yake mata. Ko baya son abu in tana so zai san yadda zai yi ya so abin. Sabir da yana tsaye yana kallon irin murmushin da take sai yaji wani dadi. Hawaye kuma ya dawo zubo mata tina in kuma ta rasa Aslam fa. Kuka sosai take yi har Sabir ya tsaya gaban ta bata ganshi ba. Handkerchief ya mika mata. Amsa tayi tana goge hawayen fuskar ta ba tare da ta ga wanda ya bata ba. Zama yayi daga gefe ya ce, "Haba *Husnah* mene na kuka kuma. Ki dauki hakuri kowa hakuri yake ki na wa Dady addu'a." Kai ta daga tare da kallon sa. Shima kallon ta yake yana sanye cikin dark blue din wando da bakar riga. Sosai yayi kyau. Murmushi ya sakar mata. Itama murmushin ta sakar masa. Hira ya fara janta yana bata abin dariya. Sun jima suna tare sannan suka shiga wajen Mami. Mami dake zaune rike da casbaha, tana ganin Asma'u ta gane tayi kuka. Murmushi tayi ta mika mata hannu tayi gun ta. Ta ce, " *Asma'un Dady* kukan ki kayi ko?" Kai ta girgiza tana murmushi. Murmushin itama Mami tayi ta ce, "Hakuri dai zamu nayi. Muma Allah bamu wucewa lafiya." "Ameen!" Suka amsa. Hira Sabir da Mami suke ita kuma tana can a whatsapp suna chat da Yaa Aslam. Hakuri yake kara bata tare da kwantar mata da hankali. Suna yi tana satar kallon Sabir kamar yadda shima yake satar kallon ta. Ita dai Sir Sabir yana burgeta, akwai shi da saukin kai ga fara'a. Haka nan nature sa na burgeta. Ido ta lumshe sai kuma fuskar Aslam ta bayyana yana mata murmurshi Itama murmushin tayi ya zame ta kwanta akan kujera. *INDABAWA* [1/18, 14:22] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* *Gidan Amanci da albarka* Dedicated to *My Lovelly Momy* *146-150* Kwanan Pretty biyu sannan ta koma gun malamin ta. Tana zuwa ya hau mata albishir da aikin ta yayi kamar me. Murna ta farayi. Malamin ya ce, "Sai dai akwai wani hanzari ba gudu ba. Shine ki kula sosai sannan kafin aure kiyi kokari ki dawo dan akwai wani abu da za a karayi miki." Godiya tayi masa, ya ce, "Kar ki damu da kin je gida zaki tadda abin mamaki." Kudi masu yawa ta zube masa ta tashi tana masa godiya shi kuwa a ransa tinda ya kusan ce ta yaji a duniya ba wacce yake so kamar ta. Yayi Alkawari da duk daren dadewa sai ya mallake ta ta zama tasa gaba daya. Ya bata dama ne ta je wajen Aslam din amman yayi alkwarin shi da kansa zai raba su dan ya same ta. Ita kuwa Pretty gida tayi tana ta murna. ********************************************** Aslam ne zaune a dakin sa yana waya da Asma'u. Duk wayar da suke kara kwantar mata da hankali yake, sosai take samun nutsuwa in tana tare da Aslam. Sai dai kwanan nan tana yawa mafarkai akan Aslam, wanda in ta zauna ita kadai tai ta kuka ta rasa kukan mene, amman tasan tana tsoron rasa Aslam ne. Kwanan nan ta dan rame ta kara rage walwala duk da yadda take so ta sake ko dan tana sawa Mamin ta nishadi amman kasawa take. Bama in da dare bayan sun ci abincin dare. Ba wanda yake fado mata sai dady shi yasa da sauri take tafiya daki ta sha kuka. In ba Aslam ne ya kira ta ya kwantar mata da hankali ba. Dan Aslam ko ta chatting yana gane a irin mood din da take bare kuma yaji muryar ta. Aslam dake kwance idon sa lumshe yana yiwa Asma'u tadi mai dadi da sanya ta nishadi har yaji tayi bacci. Wayar ya bari a kunnen sa yana jin yadda numfashin ta ke sauka a hankali a hankali. Yana kwancen nan bai tashi yayi alwala yayi shirin bacci ba bare addu'a bacci ya dauke shi. Ya jima yana baccin can kuma sai ya mike. Dakin ya fara kalla. Ba abinda yaji yana so ya ji ko ya gani in ba Pretty ba. Abokin sa Mohd da Pretty tasan shi ta dalilin sa ya kira a waya. Abokin sa dake kwance yana bacci dan lokacin wajen karfe uku ne yaga kiran sa. Dauka yayi dan shi ya zata ma ba lafiya ba. Aslam ne ya katse masa tunanin dalilin kiran sa ta hanyar ce masa, "Mohd dan Allah number Pretty nake so yanzun nan." Mohd cire wayar yayi daga kunnen sa ya kara kallon me kiran nasa. To kawai ya fada ya kashe wayar. Mamaaki yake me Aslam zai yi da number Pretty bayan ko sunan ta bai son ji bare wani abu da ya shafe ta. Baki ya tabe ya ce, "Shi yasani." Number ya tura masa ya koma bacci. Aslam kuwa yana ganin number yai ta kira amman a kashe. Ranar har asuba bai kuma ba yana ta kiran wayar. Kiran sallah shi ya sa ya hakura ya mike yai wanka yai alwala ya tafi massalaci. Yana fita Asma'u ta kira saboda jin bai kira ta ba. Amman shiru bai dauka ba. Tayi tsammanin yaje masallaci shi yasa ta bar kiran nasa. Aslam kuwa yana dawowa daga massalaci ko ta kan wayar sa bai bi ba. Ya shiga bayi ya kara wanka ya fito ya shirya cikin Wando baki sai riga ruwan kasa. Yayi kyau dashi. Turare ya dauka ya feshe jikin sa dashi. Falo ya fita ya tadda Momy na hada musu wajen karyawa. Gaisawa suka sannan ya mike ya fita kamar wanda ake hankada shi. Sauri kawai yake yaje yaga Pretty, gudu yake sosai har ya karasa gidan su, Horn yayi aka bude masa gate din fitowa yayi bayan yai parking ya akai a kira masa Pretty Wanda ya aika cikin gidan yazo ya ce, masa Pretty bata nan. Cikin mota ya koma ya zauna. Wani iri yake jin sa. Ranar ji yake in har bai ga Pretty ba bazai iya rayuwa ba. Duk ransa yana son yasan halin da Asma'u take ciki da ya fara tunanin Asma'u sai kuma Pretty ta fado masa. Duk da Asma'un ba gushewa take a zuciyar sa ba amman ya rasa dalili. Haka ya yini a harabar gidan su Pretty sallah ce kadai ke tayar da shi. Da ya dawo zai tambaya ko Pretty ta dawo. Cikin lokaci kan kani ya canja ya koma wani iri. Ranar sai karfe goma ya koma gida bayan ya tabbatar da Pretty bata nan. Jiki a salube ya dawo gida. Momy kuwa da hankalin ta ya gama tashi na ganin tin safe basuyi waya da shi ba kuma in ta kira ba ya dauka ya daga mata hankali. Yana dawowa ta hau tambayar ko lafiya. Ce mata yai bai da lafiya, wannan yasa ta kai shi daki ta hada masa ruwan wanka sanna ta kai masa abinci. Wankan yayi ya ci abinci. A ransa yana tunanin yau ko a wane hali Asma'u take. Har ya mike zai dauko waya ya kira ta kuma sai ya fasa ya koma ya kwanta. Tunanin sa daya Pretty. Haka ya kwana ya tashi. Dan ko baccin kirki bai samu yayi ba. Washe gari ma tin safe ya kuma dirar wa gidan su Pretty. Pretty kuwa tana hanya dawowa ggida ana sallah la'asar aka kawo ta kofar gidan su. Motar Aslam ta gani a cikin gidan su. Matsawa tayi wajen motar ta kalla ta kuma kalla. Tabbas motar Aslam ce kenan da gaske dai abinda Malam ya fada mata. Wani tsalle ta doka ta yi cikin gidan bangaren ta, ta shiga tai wanka ta fito tayi falon gidan. Mahaifiyar ta ce zaune cikin shigar kasaita. Tana kallo. Pretty ce ta shigo ta fada jikin ta. Kallon ta Mahaifiyar tata tayi ta ce, "Pretty ni ai nayi fushi kwana biyu ko neme na bakya yi." Kai ta dan sosa ta ce, "Sorry Mommah!" "Shikenan waye ne tun jiya yake zaryar neman ki a gidan nan." Kallon mahaifiyar tayi ta ce, "Wani ne, shine wanda nake son aura." Murmushi uwar tayi ta ce, "Kai Alhamdulilah amman naji dadi amman na bar shi a waje tin jjiya yake zarya fa." "Kar ki damu Mommah nima nasha wahala akan sa." Mommahn ta ce, "Ah ai kam kema gasa abin ki." Pretty ta mike ta ce, "Kisa a kawon abinci bangare na." Ta fice. Dakin ta ta nufa ta zauna. Wayar ta ta dauko ta kunna. Text din Aslam ne suka dinga shiga wayar. Sai da ta gama karantawa taga yadda ya hauka ce sannan ta sheke da dariya. Kiransa tayi. Lokacin yana jikin motar sa dan bai dade da dawowa daga massalaci ba. Yana ganin kiran ta yai saurin dauka. Ya ce, "Haba Baby na ina kika shiga ne haka?" Murmushi tayi ta ce, "Kana ina ne?" Gidan ya kalla sannan ya ce, "Ina cikin gidan ku fa." "Oh ai ban sani ba yanzu na dawo. Ka sa a nuna maka site dina sai ka shigo." Nan da nan ya tambaya aka nuna masa ya nufi wajen da sauri dan bai da abinda yake burin gani kamar Pretty. Tana zaune a kan kujera gaban ta kayan abinci ne kala kala. Yana shigowa ta mike ya mata masifar kyau. Yana sanye da Brown wando sai milk din riga. Wajen sa ta nufa ta kamo hannun sa. Murmushi ya sakar mata ya karaso cikin dakin. Zama sukai a kujera mai daya ta zauna akan cinyar sa. Fuskar sa take shafawa a hankali kafin ta daura kan ta a kkirjin sa. Aslam kuwa wata ajiyaar zuciya ya dinga saukewa dan ko ba komai ya samu abinda ransa ya matsa masa ya zo ya nema. Duk da zuciyar sa tana can ga Asma'u amman wani bangaren tunanin sa yana ga Pretty ya rasa dalili. Kallon sa ta danyi ta ce, "Wai da gaske kai ne?" Kallon ta yayi ya ce "Ga alama nan kuwa." Kai ta gyada ta ce, "Ya batun soyayyar mu." Wani murmushi ya saki ya ce, "Sai yadda kika ce." "Da gaske?" Ta tambaye shi tana wasa da sumar kan sa. Kai ya gyada mata. Murmushi tayi ta ce, "Aure nake so muyi nan da sati biyu." "Sati biyu kawai " Ya tambaye ta. Kai ta gyada masa, ya ce, "An gama. Nawa ne zai ishe ki siyan kayan lefe da komai da komai." Kai ta dan daga ta ce, "Ka bari zuwa gobe zan duba." "Shikenan! Ki fada min goben fa. Dan nima na matsu." murmushi tayi ta rumgume shi. Shima rumgume tan yayi. Kiss ta fara masa, jiki da jini tini shima ya hau biye mata. Kiran sallah da yaji ana yi shi yasa yai saurin tsayawa daga abinda yake yi. Mikewa yayi. Kallon sa tayi ta ce, "Lafiya?" Nuni yai mata da waje sannan ya ce, "Kiran Sallah ake." Tsaki tayi ta ce, "Ni na zata ma wani abun ne." Ta koma ta zauna Kallon ta yayi yai murmushi ya ce, "Bari naje na dawo." Ya fice ranar dai har goma suna tare da Pretty da kyar ta kyale shi ya tafi. *INDABAWA* [1/18, 14:22] Maryam S Indabawa🥰:  *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* Facebook @Maryam sulaiman Wattpad @Msindabawa Instagram @Maryam S Indabawa 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* *Gidan Amanci da albarka* Dedicated to *My Lovelly Momy* *151-155* An Kar6o Daga *Aisha (ra)* Tace: Na Tambayi *Manzon Allah(ﷺ)* Game da Waige a Cikin Sallah? Sai Yace: *"Wata Fisga ce Shedan Yakeyi a Cikin Sallar Bawa"*. (Bukhari)._ _A Hadisin *Tirmizi* Kuma Ya Ingantashi: *"Kashedinka da Yin Waiwaye a Cikin Sallah, Domin Halaka ne, Idan Ya Kasance Babu Makawa Sai Kayi, To Kayi A Cikin Sallar Nafila"*._ Yana shiga gida ya tadda Momy zaune a falo. Kallon sa tayi ya karasa gun ta. Gaishe ta yai ya dan zauna. Kallonsa tayi ta ce, "Aslam lafiyar ka kuwa. Kwana biyun nan ina kake zuwa da har kake kai dare haka a waje." Kai yayi kasa da shi. Dan ka idar sa da anyi isha'i yana gida. "Ba magana nake maka ba. Ka fadan inda kake zuwa." Shiru ya karayi. "Wallahi Aslam zan batar maka in baka fadan ina kake zuwa ba." kai ya dan sosa ya ce, "Daman ina son nai miki maganar ne, wajen wata budurwa ta wacce nake son aura nake zuwa." Tsaki Momy tayi ta ce, "Wai ni sa'ar ka ce da kake min wasa bayan kasan ba lokacin wasa bane yanzu." Shiru yayi yana tunanin ta inda zai fara. "Wai ba magana nake maka bane, ko so kake na kira mahaifin ka na fada masa." Kai ya girgiza ya ce, "Momy da gaske nake." Momy ta ce, "Da gaske kake kamar ya?" Kai ya sosa ya ce, "Momy daman mun gama maganar aure da 'yar gidan tsohon ministern man fetur ne akan nan da sati biyu zamuyi aure." Kallon sa Momy take tama kasa cewa komai. Dagowa yayi ya kalle ta, ta ce, "Eh ka dago ka kalle ni ai nifa bangane mai kake fadi ba." "Eh Mami yar sa Pretty ita nake so nake son muyi aure nan da sati biyu dan har nace ta fadawa Mahaifin ta ma." Kallon mamaki Momy kewa Aslam dan gani take kamar ba Aslam din ta ba. Aslam din ta mai hankali da nutsuwa amman ji wannan inda yake mata wani shirmen zance. Amman kuma fa zancen kamar akwai kamshin gaskiya. Da kyar Momy ta iya bude baki ta ce, "Asma'un fa?" Kai ya girgiza ya ce, "Momy ni yanzu ga wacce Nake son na aura." Kallon sa Momy tayi ta ce, "Aslam kana cikin hayyacin ka kuwa." Kai ya gyada mata. Momy ta ce, "Me ya hada ku da Asma'un taka." Kai ya girgiza ya ce, "Wallahi Momy ba komai." "Amman saboda me zakai mata haka." Kallon Momy yayi ya kasa bata amsa. Shima bai san abinda yake fadi ba. Ji yake kamar bashi yake maganar ba. "Aslam kasan me kake fadi kuwa. Asma'un taka kake son ka ce min ka fasa aura ko kuwa." Kai ya gyada mata. Momy ta ce, "Inna illahi wainna illahir rajiun." Sai da ta fada sau uku sannan ta dago ta kalli Aslam sosai dan taga ko ya fara shaye shaye ne. Har mikewa tayi tana shinshina sa da duba sa. Ganin ba alamar shaye shaye yasa ta kuma mike tayi wajen sa tana duba shi. Tabbas Aslam din ne dai 'dan ta. Komawa tayi ta zauna tana rike kan ta. Sanna ta dago ta ce, "Wallahi Aslam ba da yawu na ba a auren da kake son kayi. Ba ruwana kaje ka nemi wata uwar bani ba." Ta mike ta bar masa falon. Mikewa yayi jiki a sanyaye yayi dakinsa. Daki ne guda kai kace dakin wata amaryar ne. Babu abinda babu a ciki. Kan kujera ya fada, yana dafe kan sa. Ya zai yi. Wayar sa da tin dazu take kara ya dauko ya duba. *Soul mate* shine abinda ya bayyana akan wayar. Ajiyewa Yayi ba tare da ya dauka ba. Dayar wayar sa ce ta hau ringing itama yana dauka naga *My* ya bayyana akai. Shima ajiyewa yayi bai dauka ba. Haka ta gama kiransa amman bai dauka ba. Shi kansa wani zafi yake ji, baya son damuwar Asma'u amman mai yake damun sa yake neman sa ta a damuwa. Dan ya tabbata Asma'u tana cikin damuwa fiye da tunanin mai tunani. Har ya dau wayar zai kira sai kuma ya fasa ya kira Pretty waya sukai sosai. Dan har sha biyu suna waya sanna sukai sallama yai wanka yazo ya fada gado. Shi kansa yasan bai da lafiya. Dan rashin Asma'u ba karamin tashin hankaline a rayuwar sa ba. Pretty kuwa tana can har an fara shirye shiryen aure. Dan komai da take bukata tai masa list din su. Haka nan kudaden da za a kashe wajen taro duk ta masa suma list Sosai ta tsuga kudi dan komai na karya take so yayi mata. Waya kowa tayiwa kawayen ta kan cewa nan da sati biyu bikin ta. Dan har kalar ankon da za a sak"a ta fitar dashi. ********************************************************************* Asma'u ce kwance, akan gadon kai daga ganin ta kasan ba lafiya ba. To rabon ta da abinci kwana biyu kenan. Hankalin ta ya kasa kwanciyya da rashin kiran da Yaa Aslam bai mata ba gashi ta kira shima bai daga ba. Ta kira Momy ma ita ma bata daga ba. Tana kwance idon ta jajir dan rabon ta da bacci shima yau kwana biyu ne. Ga wata faduwar gaba da take yawan yin ta. Ta rasa ta me ce. Ido ta lumshe hawayen da ya taru suka zubo akan fuskar ta. Juyi tayi tana me fashewa da kuka. Ba wanda ya fado mata sai Dady. A duniya ta san indai Yaa Aslam ya na nan ba zatai kukan mutuwar Dady ba. To yanzu in Yaa Aslam din ya mutu tayi yaya kenan. Ko in ya barta tayi ya kenan. Tana tunanin taji an bude kofa. Da sauri ta goge hawayen idon ta. Yaa Buhari ne, ya shigo hannun sa dauke da Leda. Kan gadon ya karasa ya dan zauna kafin ya dago ta. Jikin ta ya taba yaji har lokacin da zazzabin. Kallon ta yayi ciki tausayawa ya ce, "Sannu Asma'u. Ya jikin?" Murmushi yake tai masa ta ce, "Yaya nifa yanzu normal nake ji na." "Da gaske?" Ya tambaya yana mata murmushi shima. Kai ta gyada masa. Murmushi yayi ya mika mata ledar hannun sa ya ce, "Ungo wannan to ki daure kici kinji Kanwata." Amsa tayi idon ta na kawo kwalla. Ta ce, "Tnc bro." "Ina zuwa. Akwai wani suprise da zan miki " Ya mike ya fita. Bayan sa ta bi da kallo yana fita ta fashe da kuka. Mami ce ta shigo dakin da yake Buhari bai rufe kofar ba bataji shigowar ta ba. Mami ce ta dago da kan ta ce, "Oh Asma'u ke haka zaki ta ciwo da kuka. Wai yaushe zaki daina kuka in baki da lafiya." Hawaye ta goge tana son kawar da damuwar ta. Mami ta kalle ta sosai ta ce, "Bayan zazzabin me yake damun ki. Dan ga damuwa nan fal a fuskar ki. In akan Dady ne, dan Allah ki rage damuwar nan Amsa'u kina masa addu'a kinji." Kai ta gyada. "Yauwah koke fa, *Husnahn Dady* " murmushi tayi. Mami ta dauki ledar da Buhari ya kawo mata ta bude. Murmushi tayi ta ce, "To ai ke sai ya narke" Ta fada tana zaro mata ice cream din daga leda. Daya ta mika mata ta mika.mata kullin naman da ya siyowa kowa nasa. A firij ta zuba ragowar ice cream din. Sannan ta ce, "Ina Buharin?" "Yanzu zai daw......." bata karasa fadi ba sai gashi ya shigo da sallama. "Au ina kaje?" Mami ta tambaye shi. Kallon Asma'u yayi ya ce, "Daki fa naje." Zama yayi a gefen Asma'u ya ce, "Sis an sa ranar aure na da Zainab fa dan kiji tare za ayi da naku." Yana fadar haka taji kirjin ta ya buga. Dan har sai da ta dafe shi. A zahirin gaskiya taji dadi amman kuma bata san me ya haifar mata da faduwar gaban ba. Murmushi tayi ta ce, "Kai Alhamdulilah. Amman kuma shine ba a fada min ba." "Sorry ai kece naga bakya jin dadi." "Ni ba wani nan Yaya ka sani fada min zai yi sanadiyar samun sauki na. Zan hadu da Anty Zee din ne." Murmushi Mami tayi ta ce, "Kaji har baki ya bude ko?" Daga haka suka ci gaba da hira sosai suka dauke mata kewar Yaa Aslam. Dan har sha daya suna tare. Sannan. Buhari ya tafi dakin sa. Mami kuma suka. kwana tare. Washe gari ta dan ji dama dama amman a zuciyar ta ba sauki sai abinda yyai gaba. Aslam kuwa sai ya tari Dadyn sa da maganar ko kallo bai ishe shi ba. Dan haka ya tafi gun Wan Dadyn sa. wan Dady kuma ya shige masa akan maganar auren su da Pretty. Komai da komai akai aka tsaida nan da sati uku za ai biki. Lokacin da Dadyn Aslam ya samu labari kasa magana yayi. Dan baisan me zai cewa, Amina ba shi har ga Allah yafiwa Aslam sha'awar Asma'u. Ko Momyn Aslam kasa mata maganar yayi shi kadai ya dinga juya abin a ran sa. Aslam ya kira yai masa gargadi akan ya janye batu auren yarinyar da yake son aura amman sai ga Aslam har da su kuka. Da Dady yaki sauraron sa mma sai ya zube ya suma a gun. Da sauri Dady ya fita dashi asibiti hankalin sa a tashe. *Alhamdulilah* Anan na kawo karshen littafin. *LABARIN RAYUWAR Asma'u Husnah* *Part 1* Sai ku saurare ni dan jin karashen sa. Anan ne zamuji Shin Aslam yana auren Pretty ko Asma'un yake aura. Sannan zamuji Yadda Sabir zai kasance. Anan nake muku fatan alheri tare da cewa mu hadu a *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah PART 2* Ina son naga comment sosai tukkinna. And pls don't forget to vote @MSindabawa *Nagode masoya na. Allah ya bar kauna* HHHHH YA KUKA JI. FAN ALLAH KUYU HAKURI AKAN YANAYIN LITTAFIN KOMAI A TSARE YAKE ZAKUJI DADIN SA SOSAI *Muje zuwa* YANZU AKA FARA. Godiya ga masoya masu bibiyar littafi na. Bazan manta dake ba *Ummu Ayda, fadeelat, bela'u, sis Kibdiyya, Fatitih, namesake, Asmy, Husnah, and also u Mahee Abdullahi kai kuna da yawa da yawa nagode nagode da bibiyar littaffin man da kuke. Allah ya bar kauna nagode* Muje zuwa *INDABAWA* [1/18, 14:26] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* *part 2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* *Gidan Amanci da albarka* Dedicated to *My Lovelly Momy* *Bismillahir Rahamanir Rahim* *Alhamdulilah.* Allah nagode maka da ka bani ikon fara cigaba da karashen littafin *Asma'u Husnah* Allah ina rokan ka da ka bani ikon kammala shi lafiya kamar yadda na fara lafiya. Masu korafi akan littafin kucigaba da bibiyar sa zakuyi komai. *Mahaifiya ta farin cikin rayuwa ta. Mahaifiya ta hasken idaniya ta. Allah dada lafiya da nisan kwanan Momy Ameen* Allah ka jikan *Mahaifina, da dukkan musulmai baki daya. *Kannena farin ciki na. Allah bar min ku. *Nusaiba and Hauwa'u (Yasmeen)* One love. Ina mika gaisuwa ta ban girma gare ki yar uwa Anty nah. *Rashida Abdullahi Kardam* Allah ya dafa Allah ya karawa Mama lafiya. Allah baki miji nagari da zuri'a daiyaba. Ameen. Sai sakon gaisuwa ta ga *Hajiya Nafisa* Momyn mu. Allah ya kara girma ya kara lafiya da arzuki ya Allah ya raya zuri'a. Ameen. Sai gaisuwa ga Dukkan nin yan uwa marubuta musam yan kkungiyar HAJOW tare da yan uwan abokan azurki masoya. Allah ya kare mana ku Ameen. Masoya nagode da kaunar ku a gareni nima ina kaunar ku. Allah marasa lafiya na gida dana asibiti Allah ya basu lafiya. Allah ka daukaka musulunci da musulumai. Allah ka karya kafirci da kafirce. *Ameen* Bari mu shiga cikin karashen littafin dan muji abinda zai faru. *1-5* Ganin halin da Aslam. ya shiga ba karamin dagawa Dady hankali yai ba. Amman duk da haka ya ce bai yadda Aslam ya auri Pretty ba. Aslam kuwa ba karamin tashin hankali ya shiga ba. dan jinin sa ba karamin hawa yayi ba. Momy da batasan me yake faruwa ba yasa ta shiga tashin hankali na rashin ganin Aslam ba. Dady ta tara dan ganin bata ga Aslam ba har dare. Dady ne ya fada mata duk abinda ya faru. Momy mamaki ta tsaya yi yanzu abinda Aslam ya zaba kenan. Zama Momy tayi ta dafe kan ta. Dady ne ya zauna kusa da ita ya kamo hannun ta. Kallon sa tayi idon ta jajir ta ce, "Dadyn Aslam ya zan yi da Asma'u. Kai kan ka shaidane akan soyayyar dake tsakanin su. Ban san me ya samu Aslam ba har haka ta faru. Amman ka min izini gobe na tafi kano naji me yake faruwa." "Ba komai. Ki kwantar da hanaklin ki. Na amince kije Allah ya kyauta." "Ameen!" Kwana Aslam yai a asibiti dan Dady ko wajen sa bai koma ba. Sai Pretty ya kira ya ita ta kwana a wajen sa. Washe gari Momy ta daga zuwa Kano. Asma'u ce kwance zazzabi ya rufe ta dan jikin ta kamar wuta. Sai rawar sanyi take, idanun ta sunyi jajir dashi. Mami ce ta shigo dakin rike da wani dan bowl da karamin towel a hannun ta. Zama tayi a gefen Asma'u ta yaye bargon da ta rufa dashi. Hijab din jikin ta ta cire mata ta matsa kusa da shi ta na tsoma towel din a cikin ruwan ta dauko ta matse sannan ta saka mata ajiki. Wata ajiyar zuciya ta sauke, tana mme bude idon ta da sauri. "Sannu!" Mami ta fada tana cigaba da Shafa mata ruwa a jikin ta. Sallamar Momy, Mami ta jiyo daga sama. Ajiye ruwan hannun ta Mami tayi ta mike ta fita. Ganin Momy yasa ta saki fara'a ta ce, "Anty nah Oyoyo." Ta rumgume Antyn tata. "Mu shiga dana ciki." Suka shiga dakin Mami inda Asma'u ke kwance. Momy na shiga taci karo da Asma'u kwance da sauri ta karasa wajen ta ta ce, "Asmy na lafiya?" Ido Asma'u ta bude jin muryar Momy. Da sauri ta mike tana sakin murmushi. Idon ta kamar zafin wuta saboda haka kanta yake sara mata dan har harbawa yake. Zama Momy tayi agefen ta tana kamo hannun ta. Ta ce, "Asmy bah lafiya ne?" Murmushi Asma'u tayi ta ce, "Dan zazzabi nake." Momy ta kalli Mami ta ce, "Tin yyaushe kuma amman baki fada min ba." "Yi hakuri Anty, Wallahi kwana ta uku ke nan." Kallon ta, ta maida kan Asma'u ta ce, "Sannu Baby nah. Kunje asibiti." Mami ce ta ce, "Kinsan Amsa'u ai, tana likita amman bata son shan magani." "A'ah haka bazatai yiyu ba. Tashi muje." Ta mike tana daga Asma'u Mikewa Mami tayi tabi bayan su. Asibitin Malam Aminu Kano suka tafi. Suna zuwa suka wuce Emergency. Suna zuwa suka shiga ganin likita da yake suna da hanya. BP ta ya auna, sannan ya dauki jinin ta, ya auna. Gado ya basu ya ce, sai ana mata karin ruwa. Buhari suka kira suka fada masa suna asibiti. Sosai Doctor yayi musu fadan akan me jinin Asma'u da ya ga ya hau. Mami ta rasa me yayi sanadin haka ita gani take kawai damuwar rashin Dadyn ta ce. Momy ce ta hau tunanin ko dai sun ssamu matsala da Aslam ne shiyasa hakan ta faru. Nan da nan sai ga Buhari yazo. Lokacin Asma'u na bacci. Zama sukai ranar a asibiti suka yini sai gab da magariba aka ssallame su suka tafi gida. Suna shiga gida Mami ta shiga kitchen. Asma'u kuma Momy ta hada mata ruwan wanka ta shiga tayi. Tana fitowa ta saka kayan baccin ta sannan ta tada sallah. Momy ma sallah tayi sannan ta zauna tana kallon duk wani mmotsin Asma'u. Tin aa hanya take fama da kiran wayar Aslam bai dauka ba. Yanzu ma kiran nasa ta karayi. Ganin bai dauka ba ta fara zargin ko lafiya. Wata ta ce, lafiya kalaou da ba lafiya zai kira ya fada mata. Wata zuciiyar kuma ta ce ko wayar sa aaka dauke. Nan ma ta ce da zai sanar da ita. "To ko nai masa wani abun ne?" Ta tambayi kanta. Kai ta girgiza ta ce "In haka ne da zai sanar dani." Shiru tayi tana son ta gane me yake faruwa amman ta kasa. Har akai isha'i tana zaune a inda take mikewa tayi tai sallah. Sai da ta idar tai addu'a sannan ta kalli Momy da ta idar da sallah itama. Ta ce, "Momy ya Aslam kuwa lafiya ina neman wayar sa bana samu." Kallon ta Momy ta yi ta ce "Tin yaushe kuma?" "Yau wajen kwana biyar fa rabon da muyi waya. Bayan Yaa Aslam kullum sai munyi waya dashi." Kallon ta Momy tayi ta tausaya mata ta ce, "Kuma ba abinda yya hada ku." Kai ta girgiza ta ce, "Lafiya muka rabu da shi." Kai Momy ta jinjina ta ce, "Kinga kar ki damu. Kin san ance jinin ki ya hau ki rage tunanii zan kira sa naji kinji. Ki kwantar da hankali ki." Kai ta gyada ta mike ta hau gado ta kwanta. Zuciyar ta in banda bugawa ba abinda take. Gaskiya tana son Yaa Aslam bata san inda zata sa kanta ba. Tana kwance Mami ta shigo mata da kunun da ta dama mata. Amsa tayi ta dan sha sannan ta mika mata. Kwanciyya ta koma tayi sannan ta dasa daga inda ta tsayaa a tunanin ta. Washe gari Mami da Momy suna zaune a falo. Momy ta dubi Mami ta ce, "Amina wata matsala ce ta kawo nifa." Kallonta Momy tayi ta ce, "Wacce irin matsala?" Ajiyar zuciya Momy ta sauke ta ce, "Akan Aslam da Asma'u ne." Kallon ta Mami tayi ba tare da ta gani me take fadi ba. Momy ce ta gyara zama ta fada mata duk abinda yake faruwa. Kai Mami ta jinjina tana mamaki anya Aslam ne kuwa. Mami ce ta ce, "Kinga Anty kuyi masa yadda yake so, Allah yasa haka ne mafi alheri ita Asma'u sai ta hakura." Kallon ta Momy ta yi ta ce, "Wai ke Amina meyasa ko da yaushe kike son nuna min banbanci tsakanin ya'yan nan namu ne, kina zaton in nice Asma'u tayi ba dai dai ba zan barta ne, amman ke sai ki ce Allah yasa haka ne yafi alheri. Ai nasan daman da wannan addu'a." Mami dai shiru tayi fana sauraron fadam da Momy ke mata. Sai da ta gama sannan ta ce, "Kiyi hakuri Anty amman ni ba abinda kike nufi bane, nasan tsakanin Aslam da Asma'u ba mai shiga ne, bansani ba ko wani abun ya shiga tsakanin ne ko sun samu sabani." Kai Momy ta gyada, ta ce, "Ki tuntubar min Asma'u " Mami ta ce, "Toh!" Buhari da tin da Momy ta fara bawa Mami batun yana jin su har yanzu yaji jikin sa yayi mugun sanyi. Garden yayi dan bazai iya shiga ciki ba a halin da yake ciki. Yana zuwa ya hango Asma'u kwance a kan wata kujera. Ta kudundune jikina ta. Idon ta a rufe kamar mai bacci. Juyawa yayi zai bar wajen ta mike tana kiran sunan sa. Juyowa yayi yana sakar mata murmushi, ya ce, "Ai na zata bacci kike." Kai ta girgiza masa ta ce, "Ina kwance ne kawai." Dawowa yayi ya zauna gefen ta yana kallon ta cikin tausayawa dan yanzu da ya kara jin maganganun su Momy sai ya kara tausayawa Asma'u. Kallon ta yayi dan ya bugi cikin ta ya ce, "Ina Yaa Aslam kuwa? Kwana biyu bamuyi waya ba." Murmushi ta dan ta ce, "Yana lafiya." Kallon mamakki ya bita da shi. duk yadda yaso ya bugi cikin ta bata fada masa komai ba. Haka ya hakura ya barta sai kallon tausayi da yake mata dan yasan Asma'u ta ji Aslam zai aure ba karamin damuwa zatai ba. Yasan zata iya shiga wani hali. To shi da me zai taimakawa kanwar sa kar ta shiga damuwa. Ya jima yana tunanin nan kafin ya mike ya koma cikin gida. Asma'u kuwa har lokacin number Aslam take ya kira amman No Answer. Aslam kuwa duk kiran da take masa yana gani dauka ne yake gagarar sa. Dan shima ba karamin sun dauka yake ba amman sai ya kasa. Yanzu kuwa kullum yana tare da Prety daga sune can sai sune can. Duk abinda ta lissafa tana so ya siya mata. Buhari ne kwance ya kasa gaskata abinda yaji su Mami na fadi. Mikewa yai zaune ya janyo wayar sa. Number Aslam ya kira. Bugu daya ya dauka. Gaisawa sukai kamar yadda suka saba sai dai bai tambaye sa Asma'u ba kamar yadda ya saba. Buhari ne ya ce, "Yaa Aslam daman Asma'u ce ba lafiya naji ba ka kira ya take bane." Shiru Aslam yayi na dan wani lokaci kafin ya ce, "Ai mata sannu. Yanzu ina wani aiki ne amman in na samu lokaci zan zo. kaji labarin aure na nan da sati biyu ko?" Dif Buhari yayi jin abinda Aslam ya fada. Kai ya girgiza sannan ya ce, "Au bikin naku har an matso dashi amman ban sani ba." "A'ah ba wannan ba wata xan aura anan." "Wata zaka aura!" Buhari ya fada da mamaki sosai. Aslam ne ya katse masa tunani ya ce, "Buhari kai ne dan uwana wanda kake kani a guna. Wallahi bansan me yake damuna ba. Lokaci daya naji ina son Pretty kuma ni ba son Asma'u ne bana yi ba kawai bansan me yake damuna ba." Sosai Aslam ya bawa Buhari tausayi. Tabbas yana tausayawa Aslam amman yafi tausayawa Asma'u ita da take haukan son sa. Shiru yayi. Aslam ya ce, "Dan uwana dan Allah kada hakan ya zamo sanadin yanke zumuncin mu ka fuskance ni. Momy da Dady sun kasa fahimta ta." Take Buhari ya gane Aslam ba acikin haiyacin sa yake ba. Shiru yayi kafin ya ce, "Ba komai Allah tabbatar da alherin sa." Wayar ya kashe yai shiru. Sai ga hawaye na zubowa daga idon Buhari. Tabbas dole yasan abinda zai ya kubutar da Asma'u daga damuwa. To tayaya dole ta damu in har Aslam baya kiran ta. Kuma dole ta damu in bata ganshi a wajen ta na kwanaki ba. Ya jima yana saka da warwarar yadda zai bullowa alamarin har da sai da ya samu mafita sannan ya samu sauki a ransa. Zainab ya fadawa duk halin da suke ciki sosai ta tausaywa kawar tata. Asma'u ce zaune a falon Dady ta zuba tagumi, Mami ce ta shiga ta same ta. Zama tayi a gefen ta, ta ce, "Asma'u jikin ne, Asma'u dan Allah ki rage damuwa kinji." Kai Asma'u ta daga ta zare hannun ta da tai tagumi dashi. Kallom Mami tayi ta sakar mata murmushin da bai kai zuciya ba. Mami ta ce, "Wai kuwa kin fadawa Aslam baki da lafiya.?" Shiru Asma'u ta danyi ta ce a ranta. "To ita yanzu wa zata na fadawa damuwar ta in ba Mami ba. Tinda ba Dady dole Mami ta zama kawar shawarr ta." Kallon Mami Tayi idon ta sun kawo da kwalla ta ce, "Mami bansan me yake damun Yaa Aslam ba. Kwata kwata baya kira na ko na kira sa baya dagawa. Bansan laifin da nai masa har yake hukunta ni haka ba. Mami wallahi ko bacci bana iya wa saboda ya sabar min shine mutum na karshe da nake magana dashi na kwanta bacci." Sai ta fashe da kuka. Sosai Mami ta tausayawa yar ta ta. Lallashin ta tayi sannan ta ce "Kiyi hakuri ki dage da addu'a kinsan haka na faru amman addu'a ita zata tsairatar da ke." Kai ta daga ta ce, "Mami bazan iya rayuwa ba Yaa Aslam ba. Yaa Aslam ya sabar min da son sa yadda bazan iya cigaba ba tare da shi ba." Janta jikinta Mami ta yi ta ce, "Ki daina fadar haka, ki sa a ranki ko da Aslam ko ba Aslam zaki rayuwa. Kina addu'a Allah zaba miki abinda yafi alheri a rayuwar ki." Sosai Mami ta kwantar wa da Asma'u hankali. Suna Zaune Buhari ya shigo. Ganin idanun Asma'u da hawaye ya tada masa da hankali. Zama yayi a gefen ta ya ce, "Hussyn Dady menene kuma?" Jikin sa ta fada ta fashe da kuka mikewa Mami tayi ta fita. Asma'u ce, ta ce, "Yaa Buhari. Yaa Aslam ne, bansan me nai masa ba." Ta fashe da kuka. Lallashin ta ya dinga yi. Ya ce, "Baby nah ki kwantar da hankalin ki. Ba abinda kikai masa. Kuma insha Allahu Aslam naki ne, kinji." Kai ta daga ta ce, "Yaya da Gaske." Kai ya daga mata ya ce, "Kinga ki taso muje nai miki visa ki tafi saudiya. Daga nan ki yo addu'a tinda kinga kun gama karatu. in kin dawo a bude asibiti a fara aiki. Daga nan zzan zo muje wasu kasashen kar ki damu kinji." Kai ta daga masa. Ta mike ta wanke fuska suka fita. Mami kuwa tana fita itama sai da ta dan zubar da hawayen Tana tausaywa 'yar ta. Tasan 'yar ta bata saba da son kowa ba. Da Aslam ta bude ido ta san rayuwa gashi yanzu wani al amari na shirin faruwa. Dakin da Momy ta ke ta shiga jiki a sanyaye. Kallon ta Momy tayi ta ce, "Ya kukai da ita." "Uhmm Anty ni a gani na kawai kibar Aslam ya aure wacce yake so. In yaso daga baya in Allah yayi Asma'u matar sa ce sai suyi auren. Yanzu dai ita ta ce, ba abinda ya hada su kawai dai baya kiran ta baya daukar number ta ne." "Inna illahi wainna illahir rajiun!" Momy ta dinga nanatawa. "Shiken Amina tinda haka kika ga yafi shikenan. Zan je zanyi iya bakin kokari na a daura auren nan da Asma'u amman ni ba yawu na a auren Aslam da wata." "A'ah Anty kada kiyi haka, kada ki so ma hakan ba kyau. Ki sa masa albarka kawai baki san mene alheri a rayuwar mu ba. In kika ce haka sai kiga wani abu mara dadi ya faru." Shiru Momy tayi ta ce, "Shiknan dole na tafi gida yau din man." "A'ah Anty dan Allah ki bari gobe. Kuma dan Allah kada ki tada maganar nan." Shiru Momy tayi kawai. Buhari kuwa da suka dawo gidan su Zainab ya biya da Asma'u duk dan ta samu farin ciki. Duk da jikin ta ba kwari. Ita kanta fitar da sukai ba karamin debe mata kewa tayi ba. Dan ya dan samu sanyi a ranta duk da da tayi shiru abin yake fado mata a rai. Basu dawo gida ba sai dare da siyayyar da Yaa Buhari yai mata. Kayan ta ta hau hadawa wanda za tai tafiya dasu. Sai da ta gama ta kwanta. Tana kwance nan sai tunanin Yaa Aslan ya fado mata Na yadda yake jaddada mata son sa da yadda yake kwantar mata da hankali. Kuka ta fashe da shi ta jima tana kuka sannan ta mike tayo alwala sanna ta zo ta tada sallah, Kwana tayi tana sallah tana rokar Allah ya shige mata cikin al amuransa. Washe gari da zazzabi mai zafi ta kuma ta shi. Dan ko 'kasa kasa sauka tayi. Tana kwance Momy ta shigo dakin da break din ta a hannu. Ganin ta a kwance yasa tai zaton ko bacci take wannan yasa ta fita bata tashe ta ba. Wanka taje tayi ta shirya dan ta tafi gida. Mami na falo Buhari na gefen ta ya zuba ta gumi. Ajiyar zuciya ya sauke ya kalli Mami ya ce, "Mami munje anyiwa Asma'u visa har dake ma zaku tafi tare. Amman na je na fadawa Uncle Abubakar kan a matso da biki na kusa. In lokacin ya yi Mami ke sai ki dawo. Ki bar Asma'u acan dan ta samu nutsuwa." Kai Mami ta gyada masa dan gwara Asma'u bata nan za ai bikin Aslam da ace tana nan abin bazai mata ba dadi ba. Buhari ya ce, "To Mami jibi ne tafiyar." Mami ta ce, "Allah nuna mana." "Ameen!" ya asma. Ya ce, "Asma'u bata sauko ba ko jikin ne." "Jeka duba ta. Wallahi ni bana son na ganta a irin wannan halin wallahi." Mikewa yayi yai sama. Yana zuwa ya tura kofar dakin. Tana kwance bata motsa ba. Sai da ya shiga ya zauna a gefen ta sannan ya dago ta. Idon ta ta bude wadan da sukai ja dasu. Dan wani irin ciwon kai ke damun ta wanda ya taba mata har idon ta. Dan idon ta wani zafi da nauyi yai mata. Ido ta mayar ta lumshe saboda zafin da taji yana mata. Cikin karfin haki ta ce, "Yaa Buhari ina kwana?" Bai amsa ba ya jingina ta da gado. Tea ya hada mata mai kauri sai farfesun kayan cikin da aka yi ya dinga bata a baki. Sosai taci dan rabon ta da abinci tin jiya da rana. Sai da ta koshi duk idon ta a rufe sannan ya bata magani. Mami dake ta taga tana ganin abinda suke hawaye ya wanke mata fuska. Daki ta shiga tayi kuka sosai sannan ta mike ta wanke fuska tayi dakin Asma'u. Lokacin da ya kwantar da ita kenan. Tana jin muryar Mami ta mike tana mika mata hannu. Hannun ta Mami ta kama ta kwantar da ita akan cinyar ta tana shafa kanta. A hankali a hankali har tayi bacci. Kallon ta Mami tayi. Asma'u ta rame ta kara gaske, sannan ta zama shiru shiru dan ko magana bata son yi. Hawaye ne ya zubowa Mami tai saurin gogewa. Momy ce ta shigo cikin shirin ta. Zama tayi a gefen Mami ta ce, "Amina nifa bazan zauna ina ganin Asmaa'u a wannan halin ba sannan na kasa taimakon ta. Ko ba halin da Aslam ya canja bane yasa ta a wannan halin nasan kasance war sa da ita zata rage damuwa. Zanje nasan yadda zanyi sai munyi waya," Ta mike, kallon Mami tayi ta ce, "Na miki transfer kudi, na kayan abincin wannan watan ne. Ki kula da Asma'u sai kinji ni." Momy ta fita tana kwadawa Buhari kira dan zai kai ta airport. Momy na fita Mami ta saki kuka. Su kuma tasu jarabar kenan. Allah ya dauke musu jigon su, rumfar su. Sai kuma wannan Allah ya daukewa Asma'u Aslam. "Allah ka bamu ikon cinye wannan jarabawar.' Mami ta fada tana shafa kan Asma'u. Pls don't forget to vote *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* *part 2* *INDABAWA* [1/18, 14:27] Maryam S Indabawa🥰:  *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* *part 2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* *Gidan Amanci da albarka* Dedicated to *My Lovelly Momy* Ina taaya Amrah A Mashi (Princess Amrah) murnar kammala littafin ta na (Amrah make so) Allah ubangiji ya kara basira . Siss daban kike. Ina kaunar ki saboda Allah da zuciya daya *11-15* Da yamma Mami na zaune a falo. Asma'u kwance akan cinyar ta. Zazzabin ne ya kara zafi sai hawaye da take zubarwa. Duk da ta sha magani amman jikin nan kamar wuta. Suna zaune ssuka jiyo sallamar Sir Sabir. Mami ce ta amsa masa ya shigo. Sai da suka gaisa cikin girmamawa sannan ya dubi Asma'u ya ce, "Mami yau kuma *Husnah* autan cin ne ya motsa." Tinda ya ambaci Husnah, Asma'u ta bude ido tana kallon sa. Shima kallon ta yake. Mami ce, ta ce, "Ba lafiya ne, kaga muje asibitin amman jikin kamar dada mata ciwon ake." "Ya Salam! Me yake damun ta?" Ya tambaya. "Uhmm da muka je akai mata BP sai yace jinin ta ya hau. Kaga kullum jikin da zazzabi take kwana take tashi ga ciwon kai." "Ya salam! Mami kar dai har yanzu Asma'u bata daina sa dumuwar rashin Dady ba." Mami ta ce, "To gata nan dai." "Mami dan Allah ku taso muje asibiti na duba ta." Mami ta ce, "To bari na kira Buhari." Waya ta kira shi nan da nan sai ga shi. Gaisawa sukai da Sabir sannan ya kama Asma'u suka nufi Asibiti. Office din shi kai tsaya suka nufa. BP ya kara gwada mata. Ba karamin mamaki.ya bashi ba tesult din. Dan ya tsora ta sosai. Ruwa ya kara juna mata sannan suka fita shi da Buhari ya ke fada masa yadda jinin ta hau. Buhari bai yi mamamki ba dan yasan aabinda haka ma zai iya faru da Asma'u in ya tuna irin shakuwar da soyayyar dake tsakanin Asma'u da Aslam. Magani ya kara rubuta mata. Sannan ya karbo suka dawo. Mami tana zaune ta zubawa Asma'u ido suka dawo. Maganin suka ajiye mata. Sabir ya kalle ta ya ce, "Mami ki daina sa damuwa komai zai warware. Allah zai bata lafiya." Mami ta ce, "Allah bata sauki." Tana farkawa Mami ta bata dankali ta ci. Sai magani da dakyar ta amsa ta sha. Cikin ikon Allah kafin su koma gida jikin ta ya danyi kwari. Suna komawa. Sabir yai musu sallama ya tafi gida da tunanin Asma'u a ransa. Washe gari, su Mami da Asma'u suka daga kasa mai tsarki. Momy na dira gida ta tadda Dady zaune ya zuba tagumi shima al amarin ba karamin damun sa yayi ba. Dan Aslam sai goma ko sha daya yake dawowa gida. Yanzu ko zaman hira basa yi. Sai Waya da Pretty duk yinin da suke tare. Momy ce ta zauna a gefen ta cire masa tagumin da ya zuba. Kallon sa tayi ta ce, "Dady me ya faru?" Dagowa yayi ya ce, "Komai ma. Ya su Asma'un?" Ajiyar zuciya Mami ta sauke sannan ta masa bayani duka abinda yake faru. Sannan ta daura da cewa, "Dady baka ga Asma'u ba. Wallahi bata da lafiya sosai har jinin ta ya hau. Yarinya karama Dady. Kuma na tabbata har da Aslam a sanadin wallahi." Momy ta fada ranta a bace. Ta ce, "Kaga yadda Asma'u ta rame kuwa." Dady ya ce, "Inna illahi wainna illahir rajiun. Wallahi Aslam ban san me yake damun sa ba. Amman ko jiya da nai masa magana ko aufan bai ce min ba. Ni dai abinda za'ayi kawai a daura auren nan da yana so da baya so." "Nima haka nace, amman Amina ta ce, aah abi komai a hankali. Ba asan me Allah ya tsara ba." Kai Dady ya jinjina ya ce, "Wallahi ba hannu na a cikin auren nan da yake so yayi. Nawa ido ne." Momy ma ta ce, "Nima haka amman Aslam bansan me yake damun sa ba. Allah ya shirya shi. Nasan ba kudi ke rudar sa ba ko kyau. Dan Asma'u ba za a. fada mata kyau ko ilimi ba wallahi." "Nima haka baki ga yadda nake masa sha'awar auren yarinyar nan ba. Ko dan halaiyar ta. ga ilimin ta, na tabbata bazai taba samun yarinya kamar Asma'u ba." "Ai shikenan tinda haka ya zaba Allah ya kyauta " "Ameen!" Dady ya amsa. Ya ce "Ki kira su kiji ya jikin nata." "Toh!" A lokacin ne ta buga taji sun koma asibiti ma. Sosai Momy ke tausayyawa Asma'u kuma ta dau alkawarin sai ta rama abinda Aslam yai mata. A kwana a tashi har bikin Aslam ya rage sati daya. Tin saura sati biyu kawar ta ta rakata asibiti akai mata wani dinki. Yadda zata dawo kamar budurwa. Sosai take gyara kan ta. Kamar yadda sukai da boka kan zataje in biki ya rage sati haka ce ta faru. Da taje ce mata yayi zai mata rubutu a jiki a wanke a bawa Aslam yaci a abinci ko a lemo. Ba kunya haka Pretty ta tube ya gamai mata rubutu daga nan kuma sukai masha'ar su. Sosai Pretty taji haushin bata mata aiki da yayi dan ita dan Aslam tayi. Shi kuwa bokan ta jin dadin da ta kara ya kara saukar masa da wata matsananciyar sha'awar ta. Barin ta zai yi ta dana na dan lokaci dan ya kumai wa kan sa alkawarin bazai taba barin Pretty ba sai ta zama matar sa. Haka ya kara hada mata wasu tsafe tsafen nasu sannan ta koma gida da murna. Sosai take cigaba da kara gyara kanta duk dan ta burge Aslam. A kwana a tashi har an fara shagalin bikin Aslam da Fauziyya (Pretty). Event an tsara wajen guda biyar. Sosai Aslam ya saki kudi. Momy da Dady kuwa kamar ba bikin dan ta ake ba dan ba abinda ta tsara zatai. Haka nan ko su Mami bata fadawa ba dan kar Asma'u ma ta sani. Ranta a matukar bace yake akan bikin nan dan shi kansa Aslam din tausayi yake bata. Asma'u kuwa tinda lokacin bikin Aslam.ya kama take fama da faduwar gaba. Ga wasu mafarkai da take da Aslam. Duk ta kara lalacewa, Ita aba ba jiki ba dama. dan ma addu'a da suke ita da Mami ba sanya. Dan sai su kwana suna mika kukan su ga Allah. Kullum suna waya da Buhari da Zainab haka ma Sir Sabir yana kira su gaisa. Yau ma kamar kullun bayan sun dawo daga harami tayi wanka tazo falo ta zauna. Tagumi ta saki tana tunanin Aslam lokacin da suke zaune a garden a ranar da Dadyn ta ya sanar da ita batun ya bada ita ga Aslam. Lokacin da suke zaune ya yi murmushi ya ce da ita, "Alhamdulilah nagodewa Allah.Zuciya ta ke kadai takewa na amince rike ta har abada." Asma'u ta ce, "Ya Aslam kenan!" Ya ce, "Eh! Man kada ki taba zaton zan yaudare ki" "Nasan baza ka taba bama." "Yauwah Love." Sukai murmushi a tare, "Nima Zuciya ta kai kadai take yabawa dan tasan ka riketa ba da yaudara ba." "Da gaske." "Eh!" Ta fada tana dage masa gira. ya ce, "So hadi na Allah ne, Zuciyata ke kadai ta nuna min. Na riga na sanarwa da Momy da Dady da Dady da Mami, da duk wanda muke mu'amala dasu in babu ke sai dai na rasa rayuwa ta." Ido ta zaro, "Su Momy," Eh! Mana ai kowa yasan son da nake miki in aka raba mu zan iya rasa rayuwa ta." "Allah ma ya kiyaye." "Ameen!" "Tin da Dady ya bayyana, min son ka akan kai ne, mijina baka ji yadda naji ba. Saboda Allah yasa ga wanda nake so aka hada kaga yafi dadi ko." "Shiyasa nacewa Dady kar a fada miki sai na kama bakin zaren!" "Wane zaren kuma" Ido ya kashe mata. "Zuciyar ki man. Hmmm *Husnah* baki san yadda na riki soyayyar ki a raina ba. Ta zama abin yi dare da rana. Soyayyar daraja ne da ita. Samun irin taki shine burin ko wane me hankali. Bana son na taba yin nesa dake. Kin shiga zuciya kinyo kafuwa. Ni dake babu rabuwa koman dadewa." Kallon sa ta tsaya yi. "Kai ma kasan kaine zabin rai na. Zuciya ta, ta adana soyayyar ka ba wanda ze maye gurbin ta. Sa'a ni na sama tinda na samu gwarzon masoyi kamar ka. Kai ka ke sani addu'ar neman miji na gari, kuma nasan Allah ya amsa min da ya aikon da kai a matsayin masoyi wanda nake fatan shine miji na." "Gaskiya ne. Dace da masoyi shine ribar soyayya. Nasan sabon da mukayi ni dake sai dai a kira mu tagwaye, ko yaushe in na tina ki nakanyi murmushi da jin frin ciki a cikin zuciya ta." Murmushi tayi, ta sauke ajiyar zuciya me karfin "Lafiya?" Ya tambaye ta. "Ya Aslam in na tuna da rabuwa ne sai naji zuciya ta tayi min rauni" "Haba *Husnah ba mun kashe wannan maganar ba ne." "Eh!" "To Bazamu rabu ba sai dai mutuwa itama insha Allahu tare zata dauke mu." "Allah yasa!" "Ameen." "Yauwah kinga tin yanzu sai mu fara tsara yadda bikin mu zai kasance ko?" ****---**** Kuka ta fashe da shi tina wannan hirar tasu. Ta ce, "Ni na gama amince maka Yaa Aslam amman me nai maka kake min irin wannan horan. Wallahi nasan in har nan da wani lokaci Yaa Aslam bai dawo gare ni ba komai zai iya faruwa da zuciya ta." Ta fada tana kara fashewa sa kuka. Dan a yadda take jin zuciyar ta ji take kamar zata fashe. *INDABAWA* *Asma'u Husnah* *part 2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* *Gidan Amanci da albarka* Dedicated to *My Lovelly Momy* *11-15* Da yamma Mami na zaune a falo. Asma'u kwance akan cinyar ta. Zazzabin ne ya kara zafi sai hawaye da take zubarwa. Duk da ta sha magani amman jikin nan kamar wuta. Suna zaune ssuka jiyo sallamar Sir Sabir. Mami ce ta amsa masa ya shigo. Sai da suka gaisa cikin girmamawa sannan ya dubi Asma'u ya ce, "Mami yau kuma *Husnah* autan cin ne ya motsa." Tinda ya ambaci Husnah, Asma'u ta bude ido tana kallon sa. Shima kallon ta yake. Mami ce, ta ce, "Ba lafiya ne, kaga muje asibitin amman jikin kamar dada mata ciwon ake." "Ya Salam! Me yake damun ta?" Ya tambaya. "Uhmm da muka je akai mata BP sai yace jinin ta ya hau. Kaga kullum jikin da zazzabi take kwana take tashi ga ciwon kai." "Ya salam! Mami kar dai har yanzu Asma'u bata daina sa dumuwar rashin Dady ba." Mami ta ce, "To gata nan dai." "Mami dan Allah ku taso muje asibiti na duba ta." Mami ta ce, "To bari na kira Buhari." Waya ta kira shi nan da nan sai ga shi. Gaisawa sukai da Sabir sannan ya kama Asma'u suka nufi Asibiti. Office din shi kai tsaya suka nufa. BP ya kara gwada mata. Ba karamin mamaki.ya bashi ba tesult din. Dan ya tsora ta sosai. Ruwa ya kara juna mata sannan suka fita shi da Buhari ya ke fada masa yadda jinin ta hau. Buhari bai yi mamamki ba dan yasan aabinda haka ma zai iya faru da Asma'u in ya tuna irin shakuwar da soyayyar dake tsakanin Asma'u da Aslam. Magani ya kara rubuta mata. Sannan ya karbo suka dawo. Mami tana zaune ta zubawa Asma'u ido suka dawo. Maganin suka ajiye mata. Sabir ya kalle ta ya ce, "Mami ki daina sa damuwa komai zai warware. Allah zai bata lafiya." Mami ta ce, "Allah bata sauki." Tana farkawa Mami ta bata dankali ta ci. Sai magani da dakyar ta amsa ta sha. Cikin ikon Allah kafin su koma gida jikin ta ya danyi kwari. Suna komawa. Sabir yai musu sallama ya tafi gida da tunanin Asma'u a ransa. Washe gari, su Mami da Asma'u suka daga kasa mai tsarki. Momy na dira gida ta tadda Dady zaune ya zuba tagumi shima al amarin ba karamin damun sa yayi ba. Dan Aslam sai goma ko sha daya yake dawowa gida. Yanzu ko zaman hira basa yi. Sai Waya da Pretty duk yinin da suke tare. Momy ce ta zauna a gefen ta cire masa tagumin da ya zuba. Kallon sa tayi ta ce, "Dady me ya faru?" Dagowa yayi ya ce, "Komai ma. Ya su Asma'un?" Ajiyar zuciya Mami ta sauke sannan ta masa bayani duka abinda yake faru. Sannan ta daura da cewa, "Dady baka ga Asma'u ba. Wallahi bata da lafiya sosai har jinin ta ya hau. Yarinya karama Dady. Kuma na tabbata har da Aslam a sanadin wallahi." Momy ta fada ranta a bace. Ta ce, "Kaga yadda Asma'u ta rame kuwa." Dady ya ce, "Inna illahi wainna illahir rajiun. Wallahi Aslam ban san me yake damun sa ba. Amman ko jiya da nai masa magana ko aufan bai ce min ba. Ni dai abinda za'ayi kawai a daura auren nan da yana so da baya so." "Nima haka nace, amman Amina ta ce, aah abi komai a hankali. Ba asan me Allah ya tsara ba." Kai Dady ya jinjina ya ce, "Wallahi ba hannu na a cikin auren nan da yake so yayi. Nawa ido ne." Momy ma ta ce, "Nima haka amman Aslam bansan me yake damun sa ba. Allah ya shirya shi. Nasan ba kudi ke rudar sa ba ko kyau. Dan Asma'u ba za a. fada mata kyau ko ilimi ba wallahi." "Nima haka baki ga yadda nake masa sha'awar auren yarinyar nan ba. Ko dan halaiyar ta. ga ilimin ta, na tabbata bazai taba samun yarinya kamar Asma'u ba." "Ai shikenan tinda haka ya zaba Allah ya kyauta " "Ameen!" Dady ya amsa. Ya ce "Ki kira su kiji ya jikin nata." "Toh!" A lokacin ne ta buga taji sun koma asibiti ma. Sosai Momy ke tausayyawa Asma'u kuma ta dau alkawarin sai ta rama abinda Aslam yai mata. A kwana a tashi har bikin Aslam ya rage sati daya. Tin saura sati biyu kawar ta ta rakata asibiti akai mata wani dinki. Yadda zata dawo kamar budurwa. Sosai take gyara kan ta. Kamar yadda sukai da boka kan zataje in biki ya rage sati haka ce ta faru. Da taje ce mata yayi zai mata rubutu a jiki a wanke a bawa Aslam yaci a abinci ko a lemo. Ba kunya haka Pretty ta tube ya gamai mata rubutu daga nan kuma sukai masha'ar su. Sosai Pretty taji haushin bata mata aiki da yayi dan ita dan Aslam tayi. Shi kuwa bokan ta jin dadin da ta kara ya kara saukar masa da wata matsananciyar sha'awar ta. Barin ta zai yi ta dana na dan lokaci dan ya kumai wa kan sa alkawarin bazai taba barin Pretty ba sai ta zama matar sa. Haka ya kara hada mata wasu tsafe tsafen nasu sannan ta koma gida da murna. Sosai take cigaba da kara gyara kanta duk dan ta burge Aslam. A kwana a tashi har an fara shagalin bikin Aslam da Fauziyya (Pretty). Event an tsara wajen guda biyar. Sosai Aslam ya saki kudi. Momy da Dady kuwa kamar ba bikin dan ta ake ba dan ba abinda ta tsara zatai. Haka nan ko su Mami bata fadawa ba dan kar Asma'u ma ta sani. Ranta a matukar bace yake akan bikin nan dan shi kansa Aslam din tausayi yake bata. Asma'u kuwa tinda lokacin bikin Aslam.ya kama take fama da faduwar gaba. Ga wasu mafarkai da take da Aslam. Duk ta kara lalacewa, Ita aba ba jiki ba dama. dan ma addu'a da suke ita da Mami ba sanya. Dan sai su kwana suna mika kukan su ga Allah. Kullum suna waya da Buhari da Zainab haka ma Sir Sabir yana kira su gaisa. Yau ma kamar kullun bayan sun dawo daga harami tayi wanka tazo falo ta zauna. Tagumi ta saki tana tunanin Aslam lokacin da suke zaune a garden a ranar da Dadyn ta ya sanar da ita batun ya bada ita ga Aslam. Lokacin da suke zaune ya yi murmushi ya ce da ita, "Alhamdulilah nagodewa Allah.Zuciya ta ke kadai takewa na amince rike ta har abada." Asma'u ta ce, "Ya Aslam kenan!" Ya ce, "Eh! Man kada ki taba zaton zan yaudare ki" "Nasan baza ka taba bama." "Yauwah Love." Sukai murmushi a tare, "Nima Zuciya ta kai kadai take yabawa dan tasan ka riketa ba da yaudara ba." "Da gaske." "Eh!" Ta fada tana dage masa gira. ya ce, "So hadi na Allah ne, Zuciyata ke kadai ta nuna min. Na riga na sanarwa da Momy da Dady da Dady da Mami, da duk wanda muke mu'amala dasu in babu ke sai dai na rasa rayuwa ta." Ido ta zaro, "Su Momy," Eh! Mana ai kowa yasan son da nake miki in aka raba mu zan iya rasa rayuwa ta." "Allah ma ya kiyaye." "Ameen!" "Tin da Dady ya bayyana, min son ka akan kai ne, mijina baka ji yadda naji ba. Saboda Allah yasa ga wanda nake so aka hada kaga yafi dadi ko." "Shiyasa nacewa Dady kar a fada miki sai na kama bakin zaren!" "Wane zaren kuma" Ido ya kashe mata. "Zuciyar ki man. Hmmm *Husnah* baki san yadda na riki soyayyar ki a raina ba. Ta zama abin yi dare da rana. Soyayyar daraja ne da ita. Samun irin taki shine burin ko wane me hankali. Bana son na taba yin nesa dake. Kin shiga zuciya kinyo kafuwa. Ni dake babu rabuwa koman dadewa." Kallon sa ta tsaya yi. "Kai ma kasan kaine zabin rai na. Zuciya ta, ta adana soyayyar ka ba wanda ze maye gurbin ta. Sa'a ni na sama tinda na samu gwarzon masoyi kamar ka. Kai ka ke sani addu'ar neman miji na gari, kuma nasan Allah ya amsa min da ya aikon da kai a matsayin masoyi wanda nake fatan shine miji na." "Gaskiya ne. Dace da masoyi shine ribar soyayya. Nasan sabon da mukayi ni dake sai dai a kira mu tagwaye, ko yaushe in na tina ki nakanyi murmushi da jin frin ciki a cikin zuciya ta." Murmushi tayi, ta sauke ajiyar zuciya me karfin "Lafiya?" Ya tambaye ta. "Ya Aslam in na tuna da rabuwa ne sai naji zuciya ta tayi min rauni" "Haba *Husnah ba mun kashe wannan maganar ba ne." "Eh!" "To Bazamu rabu ba sai dai mutuwa itama insha Allahu tare zata dauke mu." "Allah yasa!" "Ameen." "Yauwah kinga tin yanzu sai mu fara tsara yadda bikin mu zai kasance ko?" ****---**** Kuka ta fashe da shi tina wannan hirar tasu. Ta ce, "Ni na gama amince maka Yaa Aslam amman me nai maka kake min irin wannan horan. Wallahi nasan in har nan da wani lokaci Yaa Aslam bai dawo gare ni ba komai zai iya faruwa da zuciya ta." Ta fada tana kara fashewa sa kuka. Dan a yadda take jin zuciyar ta ji take kamar zata fashe. *INDABAWA* [1/18, 14:28] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* *part 2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* *Gidan Amanci da albarka* Dedicated to *My Lovelly Momy* *Last page nayi mistaking wajen page number zan sa 6-10 na saka 11-15 ayi hakuri wannan shine 11-15 wancan 6-10 ne nagode* MASOYA MASU BIBIYAR WANNANN LABARIN NAGODE KWARAI DA GASKE. ALLAH BAR ZUMUNCI. COMMENT DIN KU NA DADA MIN KWARIN GWIWA NAGODE. *11-15* Kuka ta kuma fashewa da shi ta ce, "Meyasa? meyasa? Meyasa yaa Aslam? Me nayi maka da na cancanci haka." Ta kuma fashe wa da kuka dan har numfashi ta na sarkewa. Mami ce ta fito ta tadda ta a hankalin da take ciki. Da sauri ta karassa gun ta. Ina har numfashin ta ya dauke Da sauri Mami ta kira suka tafi da Asma'u asibiti. Aslam kuwa ana can yau daurin aure. Duk da yau take ranar farin ciki a gunsa amman sai akasin haka. Dan damuwa sosai ya shiga na tinawa da tini da Asma'u ake daura auren nasu. Duk yadda yaso yai farin ciki ya kasa. Abokan sa kuwa dayawa duk basu je daurin auren ba dan ya riga ya koya musu son Amsa'u. Dukkan su mamaki suke sosai. Wasu kuma haushin Pretty suke ji. Wasu daga cikin abokan sa su suka hallaci daurin auren. Bayan an gama reception ya koma gida ne ya kwanta a daki. Ba abinda yake gani sai Asma'u da ke masa murmushi. Ido ya lumshe, ya rasa me yake damun sa. Gani yake kamar a mafarki wai ya auri Pretty. Mamaki yake sosai amman kuma sai wani abu ya dauke hankalin sa daga wannan. Haka da dare aka kai amarya gidan ta. Dan Mami ta ce bazai saka kowa a gidan da ya gina dan Asma'u ba. Wani daga cikin gidan shi yasa aka gyara akai wa Pretty kafin kayan ta. Amarya kamar ba amarya ba dan mayafi ma a kafada ta yafa aka raka ta gidan ta. Aslam kuwa lokacin yana gida a kwance ya rasa me zai yi. Mami da kanta taje ta same shi a daki. Duk da ganin yanayin da yake ya bata tausayi amman hakan bai sa ta ce, "Ka tashi ka tafi gidan ka. Ga amaryar ka can an kai maka ita." Shiru yayi kamar bazai yi magana ba. Sai kuma ya sauko daga kan gadon ya durkusa a gaban ta ya ce, "Momy dan Allah ki yafe min. Momy wallahi ban san abinda yake damu na ba." Kai Momy ta dauke, Kuka ya saka yana nema yafiyar Momy. Kallon sa tayi ta tausaya masa ta ce, "Ba komai kaje Allah bada zaman lafiya. Amman har ga Allah bana son auren nan naka." Kin sakin ta tayi sai da Momy ta daga sa tace, "Kaje ka shirya dare nayi." Mikewa yayi ya shiga bandaki. Ya fito ya shirya cikin sky blue din shadda. Yayi masifar kyau. Wanka da turare yayi sannan ya fita falo. Momy bata nan dan haka yayi bangaren ta. Ko da ya taba kofar a rufe take. Dan haka ya juya ya fice, motar sa ya dauka ya fice daga gidan. Gidan shi ya wuce kai tsaya. Gidan ne babba wanda yake dauke da babban falo sai kofa da take kallon gabas ita ce in an bude za a shiga bangaren Pretty, Da katon falo sai bed room guda biyu da kitchen da bandaki. Gidan yayi kyau sosai. Sai dayar kofar dake kallon ta Pretty shine bangaren Aslam benene. Shima katon falo ne sai Bed room guda biyu kamar yadda bangaren Pretty yake. Sai wajen gidan kato ne, dan bayan gidan da an shakatawa ba kamar dayan gidan da yake da komai dan har garden da swimming pool ne a shi. Zama yayi dadi tsakanin ango da amarya sai dai sabin halaye. Da yadda ya same ta. Ta maida Aslam kamar bawan ta dan sai abinda ttace shi yake mata. In ta ce, kaza dole yayi shi. haka in ta aiki shi da gudun sa yake zuwa. Duk da wani lokacin yana mamakin sa in ya kudurce a ransa bazai ba sai ya kasa. Kamar ko da yaushe yau ma gefen karfe biyun dare ya zame jikin sa daga na Pretty. Bandaki ya shiga yai wanka ya dauro alwala. Sallah yazo ya dinga yi dan sai gab da asuba ya zauna yana karanta alkur'ani. Ana kiran asuba kuma ya mike ya tafi massalaci. Bai dawo ba sai karfe bakwai. Amman har lokacin Pretty ko mikewa batayi ba bare ta yi sallah. Gidan dai yan aiki suna ta gyara shi. dan yan aikin da tazo dasu sunfi hudu kowa da aikin sa. Daga mai gyara mata turaka sai mai gyara mata kitchen da girki. Sai mai mata gyaran jiki da mai mata wanki under wears din ta. Sai wani yaro dake mata sharar harabar gidan. Ita ba abinda take sai dai a kawo mata taci ta koshi ta kwanta. Dan ba abinda ttake yi. Daga zama sai kallo sai kuwa fita yawo. Dan wani lokacin ta fice tin safe sai dare take dawowa. Aslam kuwa da yake ba gwanin cin abincin masu aiki ba sai dai yaje gida ya ci. Haka yake rana da dare. Duk ya rame ya zama wani iri da shi. Ita Momy ma tausayi yake bata. Haka shi da baya son hayaniya dan gayu ya tsara yadda zai na jin dadi da matar sa. Sai dai ya dawo ya tadda uwar lalaci a kwance yan aiki suna mata tausa. Ko wani lokacin ya dawo ya tadda bata nan. Bangaren Asma'u kuwa sai da tayi jinya sosai a makkah dan sai da Buhari da sir sabir suka je duba ta. Sai da tayi sati biyu a asibiti sannan aka sallamo ta. Ranan tana daki a kwance. Mami da Sir Sabir da Yaa Buhari suna falo suna hira. Sir Sabir ne ya tambayi mene ya jawo wa Asma'u hawan jini haka. Shiru Mami tayi kafin ta bashi labarin komai. Sir Sabir sosai ya tausayawa Asma'u duk da yana mai godiya da Allah wata kila rabon sa ce shiyasa Allah yayi ba ai auren ta ba. Daman ance, *Matar mutum kabarin sa* in Allah yayi rabon sa ce shikenan. Sir sabir ya ce, "Mami yanzu kina nufin Aslam yai aure?" A kunne Asma'u kenan lokacin da ta fito daga daki. Faduwar ta kawai suka ji. Da gudu sukayi wajen ta. Nan da nan suka kara daukar ta sai asibiti. Da kyar suka samo numfashin ta ya dawo dai dai. Dr sai fada suke dan zuciyar ta da kamo da ciwo. Banda jinin ta da ya hau. Ya ce, "Allah yasa ta tashi lafita dan ba karamin hawa jinin ta yayi ba." Kuka Mami ta dinga Sir Sabir ne mai lallashin ta dan Yaa Buhari ma ya rasa me yake masa dadi. Abinda baya so Asma'u taji kenan ya baro ta daga kano amman dai da taji. Wata zuciyar kuma ta ce, "Shikenan yanzu ai komai jjuj zo da sauko tinda ta san komai." Sai da tai kwana uku a kwance kamar gawa. Dan likita yai mata allurar da zata sa ta sami hutu ko nutsuwar ta zata dawo. Kwanata hudu sannan ta farfado shima da kuka. Dan sai a lokacin ta samu damar kuka. Ba karamin tashi hankalin ta yayi ba. Asma'u kuka take kamar ranta zai fita. Mami ce ke lallashin ta. Asma'u ta ce, "Mami me nai wa Yaa Aslam? Anya Mami. Mami wallahi ba Yaa Aslam dina bane sai dai wani Yaa Aslam bazai taba yi min haka ba. Mami Yaa Aslam da ya ce min 'yai min alkawari bazai guje min ba. Ya ce, In dai soyayyar sace na gama samu, kuma insha Allahu babu kishiya. Mami amman kuma shine yayi aure ya manta da duk alkwarin da ya sabar min dasu. Mami ce min yayi fa, 'in bar tsoro, in sanya a rai na za ayi auren mu. In Allah ya yadda zamuyi rayuwa, matsayin ma aurata za muyi shakuwa. Ba gudu ba ja da baya sona zai tayi zai zauna dani har karshen rayuwa. Mami amman ji ya guje ni. Mami shiyasa nace miki Yaa Aslam bazai taba bari na ba." Sai kuma ta fashe da kuka. Dan har numfashashin ta ya fara dauke wa dan sai da aka kira Dr yai mata allurar bacci sannan aka samu tayi shiru. Sosai Asma'u ta kuma ramewa. Ta kuma zama shiru shiru da ita dan magana ma ba sonyi take ba. Yau kamar kullum tin da aka sallamo su a asibiti take kuka su koma gida kawai tinda abinda aake boye mata ya fito fili. Sosai take rigima dan yanzu rigima ta dada yawa haka kawai sai ta tasa Mami a gaba tana mata shagwaba. To yanzu ma tana kwance a falo sai tunani take, bama lokacin da suke zaune da Dadyn ta, Dadyn ta ya fado mata da inda yake Tambayar ta abinda take bukata na bikin ta. Ta ce. "Dady da sauran lokaci fa." Dadyn ya ce "Haka ne, amman na fison komai na gama shi da wuri dan bamu san me lokaci zai bayar ba " "Haka ne Dady. Amman ni bana bukatar komai." "Kin tabbata?" "Eh Dady." "Shikenan na miki transfer din kudi ta account din ki kingan su." Kai ta girgiza ta ce, "A'ah!" "Ki duba wayar ki, zaki gani. Dan haka ki ajiye in lokacin bikin yazo in kina bukatar kudi ki huta ba sai kin hau tambayar Mami ko Yayun naki ba." Murmushi tayi ta ce, "In ban tambaye su ba ai ina da Dady ko?" "haka ne! Kina da Ni amman in ina nan ba." Murmushi tayi ta ce, "Dady tafiya zaka yi ne?" Kai ya girgiza ya ce, "Ko daya in na mutu nake nufi." Damuwa ce ta sauka akan fuskar Asma'u sosai har ta kasa furta komai. Dady ya ce, 'Haba *Husnahn Dady* mene na bata rai dan na fadi abunda dole ne ya faru. Ki daina sa damuwa aranki nasan ko na mutu kina da masu rike ki amana. Amman mutuwa tana kan kowa. Kowa lokaci yake jira da tazo kuma bata jira dauka kawai take. Gara duk abinda zamu nayi muna tunawa da ita. Kuma muna sawa a ran mu a ko da yaushe zaata iya zuwa ta dauke mu. Ki daina damuwa. Allah shi ya tsara mana rayuwar mu kuma in yai nihar mutun ya rayu sai kiga ya shekara nawa ma bai mutu ba. Ina iyayen mu duk sun mutu to muma haka wata rana zamu tafi. Fatan mu da addu'ar mu Allah yasa mu cika da imani kuma Allah yasa can ta fi nan Hawayen idon ta ta goge ta ce, 'Allah sarki ashe Dady mutuwar kuwa zakai da gaske ke." Sai maganar sa ta karshe da ya ce, ' *Husnah* dan Allah kar ki manta kina sa ya'yan ki suna min addu'a.' 'Insha Allahu. Dady ka daina sa wannan a ranka. Kai ma zaka rayu da su. Su sanka insha Allahu.' Tana tunawa ta goge hawayen idon ta ta ce, "Dady Yaa Aslam ya juyan baya bansan me nai masa ba." Sai wani kukan jin kanta na ciwo yasa tai shiru ta lumshe ido kawai. *Allah sarki Husnah Brodas nd sisters ya kk na sameku lpy. Kuyi hakuri kuci gaba da kasancewa dani. Komai na duniya yana da darko da karshe. Ko wane tsanani yana tare da sauki. Bawa bay gujewa kaddara ubangiji. Sai dai muyi ta addu'a Allah daura maba abibda zamu iya. Nagode da kaunar ku. Nima ina kaunar ku. Ina barar addu'ar ku. Kwana biyu kai na na matsamin da ciwo. Dan Allah kusani a addu'a Allah ya yayewa musulmai baki daya. Ameen. Nagode *INDABAWA* [1/18, 14:28] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* *part 2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* *Gidan Amanci da albarka* Dedicated to *My Lovelly Momy* *21-25* Tana kwance Sabir ya shigo. Zama yayi ya zuba mata ido. Sunan ta ya kira ganin alamar ba bacci take ba. Ido ta bude wanda sukai jajir dasu. "Subhanallah!" Ya fada da sauri yana matsowa wajen ta. Kallon ta yai ya ce, "Jikin ne?" Kai ta girgiza. Ya ce, "Kuka ko?" Kasa tai da kan ta. Shiru yayi kafin ya ce, "Haba *Husnah!* " Da sauri ta dago kanta. Tinawa da mutum biyu ke yawan kiran ta da sunan gashi basa tare. Daga Dadyn ta sai Yaa Aslam. to Dady ya mutu, Yaa Aslam baya tare da ita. Ashe zata kara samun wanda zai kira ta da wannan sunan da tafi jin dadin sa akan ko wanne. Kallon ta shima yake ido cikin ido. Kasa tai da idon ta, tana kokarin mai da kwallar da ta fito mata. Magana ya farai mata cikin sanyi wanda taji kamar Yaa Aslam ne ke lallashin ta. Ya ce, "Ki daina kuka. Kina godewa Allah akan duk abinda ya faru dake. Jarrabawa d Allah ke miki in kika cinye baki san wane tukwici ne zai biyo gare ki ba. Kina sa hakuri da dangana a zuciyar ki Allah zai miki sauyi da mafi alheri da izinin Allah. Kai ta daga. Tana jin sanyi a ranta kamar yadda Yaa Aslam ya sabai mata. Ya ce, "Walalhi in na gan ki cikin halin damuwa ina finki shiga damuwar." Da sauri ta dago ta kalle shi. Dan sai taji kamar Yaa Aslam dan shi yake fada mata wannan kalmar. Kasa yai da kai dan baisan lokacin da ta fito daga hakin sa ba. Hira ya dinga bata. Dan har da su dariya tana rike ciki tsabar dariya. Mami ce ta fito ta same su a haka. Dadi taji ganin yadda Sabir ke sa mata auta tayi dariya. Zama Mami tayi ita ma ana yi da ita har Buhari shima ya fito aka dinga yi da shi. Sosai ta rage damuwar da take ciki. Amman da magariba kuma sai ta sawa Mami daru kan su koma gida ta fara aiki a asibitin ta. Sosai Mami taji dadi da taji Asma'u na son fara aiki dan da ko maganar sa batayi. Ai kuwa cikin satin su ka daga suka yo Kano. Gidan ssu a gyare dan masu aikin su sun gyare masu shi. Kowa dakin sa ya shiga yai wanka suka fito suka ci abincu. A falo suka bbaje ana hira. Can Asma'u ta ce, "Bro saura wata nawa bikin ne?" Murmushi yayi ya ce, "Wata daya fa!" Ido ta zaro ta ce, "Wallahi da ba dan Anty zee zaka aura ba da ba inda zamu kara tafiya. Kiji fa Mami da ya fada mana muje mu hado kaya kafin mu dawo amman yaki ko?" Murmushi Mami tayi. amsa'u ta ce, "Mami nan da sati fa zamuje mu hado wani sati mai zuwa kuma akai kaya." Mami ta ce, "Duk yadda kika ce." Asma'u ta kalli Mami ta ce, "Na kuwa bude asibiti na hau tafiya kuma." Mami ta ce, "Me zai hana." "Shikenan. Allah Yaya ina kara fada maka dan Anty Zee ce da ba inda zani." Murmushi yayi ya ce, "Godiya nake? Nawa kuke bukata." Hararar sa Asma'u tayi ta ce, "Ai ATM zaka bamu kawai sai yadda kaga saura." Dariya yayi ya ce, "Mami dan Allah a dan tausya min dan naga wannan kanwar tawa so take ta sa na rasa ko na shinkafa ne." Dariya Amsa'u tayi ta ce, "Ai da sauki in dai na shinka fa ne, zan dire maka kayan abincin shekara ma." Sukai dariya gaba daya. Cikin ikon Allah a satin akai bikin bude asibitin. Inda suka dauke kwararun ma'aikata. Sosai ake aiki dan asibitin ya karbo. Sunan Dady ta saka wa asibitin aka saka masa. *Suleiman Specialist Hospital* Taimako sosai yake a asibitin dan har ragi take na kudin marasa lafiya. Sati daya da bude asibitin tafiyar su ta kama. Komai ta bari a hannun Yaa Buhri. Inda suka tafi ita da Mami. Sosai ta dinga jidowa Zee kaya masu kyau da tsada. Set biyu suka hado mata sannan suka hado na fitar bikin su. A lokacin ne Asma'u ta sha kuka tinawa da tai ita ma fa wai nata na nan ko. Sai ta tuna lokacin da take gwada kayan da zasu yi fitar biki da Momy ta kawo mata. Kuka sosai take sai da Mami ta shigo ta tadda ta. Mami tasan me ya sata kuka dan haka hakuri ta dinga bata. Kwanan su shida suka juyo suna dawowa suka sanar da Uncle Abubakar shi ya sanar da Dadyn Aslam da uncle iliyasu akafadawa Gidansu Zainab. Aka kai laife aka sa biki sati biyu masu zuwa. Tinda Asma'u ta dawo ta kuma komawa shiru shiru. Daga wajen aikin ma sai ta kulle a office tai ta kuka. Haka biki ya dinga karatowa. Ta dibi dinkinsu takai musu. Sir Sabir ne ya ce, zai na taya ta yin aiki. Wanna yasa ya koma asibitin ta. Yana dan taimaka mata in bai da aiki da yawa. Tana zaune a office din ta. Ta saka wani yellow material sai blue din mayafi da tayi rolling dinshi. Tayi kyau sosai ta saka blue din sandal da blue din jaka. Aiki take yana duba abu a system din ta. Kamar kullum yau ma Yaa Aslam ne ya fado mata. Kai ta kifa kanta a benci tana ta kuka. Da sallama ya shigo office din nata. Wanda ya haduwar kai ba zaka ce office bane. Sai kamshi da sanyi AC ke ratsa shi gefe TV na aiki. Sanye yake da blue din shadda yayi kyau dashi. Kansa ya saka hula hannun sa daure da bakin agogo. Kafar sa sanye da bakin takalmi. Yayi kyau sosai duk wacce ta kalle shi sai ta so shi. Har ya zauna bata san da shigowar sa ba. Ganin bata san ya shigo ba yasa ya mike ya matsa kusa da bencin ta. Dan bubbugaga table din ta take, yayi tai saurin dagowa idon ta da hawaye. Kallon ta ya tsaya yi. Ran sa abace. Ganin sa yasa ta fara kokarin goge hawayen ta. Zama yayi ya ce, " *Husnah* ke fa bakya ji ko? Wai bakya son lafiyar ki ne, kita sa damuwa a ranki. To in ba ki damu da rayuwar ki ba ni na damu da ita. In bakya son cigaba da rayuwa ki ina son kici gaba da ita dan wani ne farin cikin ki ni kece farin ciki na. kece farin ciki na. Kece buri na." Sai kuma yai shiru. Kallon da take da mamaki a fuskar ta. Kai ya gyada mata ya ce, "Eh! Wallahi *Husnah* tin san da na fara ganin ki naji ina son ki. Son ki tin a lokacin ya shige ni. Na rasa ta yadda zan sanar dake ne. Ki bani dama *Husnah* zan yaye miki dukkan damuwar ki zan maye miki gurbin Aslam da yaddar Allah." Kai ta girgiza ta ce, "Sir baza ka iya ba. Kasan waye Yaa Aslam a guna kuwa. Duk da abinda yai min jin sa nake har yanzu yana zuciya ta. Jin sa nake a rai na. Kasan tin ban san kai na ba Yaa Aslam ke so na. Da son sa na girma da son sa na san wace ni. Da shi kadai na taba soyayya. Sir ko ban auri Yaa Aslam ba to nasan bazan kara soyayya ba. Bazan taba daina son sa ba. Son sa ya riga ya zama jinin jiki na raba ni da shi bazai taba yiyuwa ba. Kayi hakuri nagode da soyayyar ka." Ta mike tana goge hawayen ta tana gogewa yana kara zubo mata. Jakar ta, ta dauka ta fita daga office din da sauri. Yanzu ita tasan soyayyar maso wani take. Tinda ita take son sa shi kuma baya son ta. A haka ta shiga motar ta, tayar da motar tayi ta nufi gidan su zee dan yin rabon kati da zasu fara. Tana shiga ta gaida Maman Zainab sannan ta shige cikin dakin ta. Tana kwance tana waya da Yaa Buhari sai soyayya suke yi. Asma'u kuwa na zaune abin duniya ya isheta. Jin hirar da Zainab take a waya shi yasa ta fara zubar da hawaye. Wacce soyayya ce bata samu ba. Amman yanzu ita ce a halin soyayya ta juya mata baya. Tana son Yaa Aslam baza ta taba daina son sa ba. Dan addu'a take Allah ya cire mata son sa amman sai son sa dake daduwa. Bata san lokacin da Zainab ta gama wayar har ta zo gaban ta ba. Sai da ta dafa ta sannan ta dago kanta. Damuwa fal a fuskar Zainab ta ce "Haba Asmmy mene kuma?" Hawayen ta goge ta ce, "Kar ki damu. Ina kati nan. Ina son zan kaiwa Maimuna yau dai naje gidan su." Kai Zainab ta gyada mata ta ce "Karfe biyu ai dai kya yi sallah kici abinci sai muje ko?" Mikewa tayi ta shiga bandakin dake cikin dakin. Alwala tayo tazo tai sallah ta ci abinci sannan ta mike. Mikewa Zainab tayi suka fita. Duk inda suka san da yan class dinsu sai da suka kai musu. A hanya Asma'u ta ce, "Wato baza ki zo ki karbi aiki ba sai kinyi aure ko?" Kai ta gyada mata ta ce, "Ki bari naje na gama cin amarci na tukkuna sai na fara. Yanzu haka kawai a ban hutun sati biyu mai naci." Kwafa Asma'u tayi ta ce, "In ma zan baki ba." Dariya Zainab tayi ta ce, "Oh sai kin bani. kinsan zan iya tafiya ta ai ba tare da an ban ba ko My husband yazo ya amsar min. Ko Mami nah ta ce na je na huta." Duka Asma'u ta kai mata ya ce, "Wallahi yarinyar nan kin min wayo." Zainab ta ce, "Wace yarinyar? Anty dai." Suka sa dariya. Daga nan suka wuce gidan su Maimuna. *INDABAWA* [1/18, 14:29] Maryam S Indabawa🥰: LABARIN RAYUWAR *Asma'u Husnah* *part 2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* *Gidan Amanci da albarka* Dedicated to *My Lovelly Momy* *26-30* Sabir kuwa tinda Asma'u ta fita ta bar shi da tunani kala kala. Allah ya sani yana son Asma'u kuma yana son ya aure ta. Mikewa yayi ya rufe mata office din shima ya fita ya tafi gun Buhari suna shirye shiryen biki. Washe gari da safe Buhari ya dau hanyar Abuja a mota Asma'u yau ma daga Wajen aiki ta wuce Gidan su Zainab. Yaa Buhari ya isa Abuja lafiya. Momy sai nan nan take da shi. Ta cika masa gaban sa da kayan abinci kala kala. Suna zaune suna hirar su Mami. Tana kara tambayar sa ina 'yar ta. Da yake haka take kiran Asma'u. Buhari ya ce, "Tana nan ai su Asma'u an zama busy daga wajen aiki sai shirye shiryen biki. Dan cewa tayi dama sai bayan biki aka bude. Damuwa dai ba laifi ta rage ta duk da tana cikin ta mu take nunawa ba ta cikin ta." Mami ta girgiza kai ta ce, "Allah sarki. Allah kawo miji na gari. Ni ina tunanin ma na samo mata miji da kaina dan na wuce haushin da aka bamu." Dariya Buhari yayi ya ce, "Haba Momy." Momy ta ce, "Wallahi." Buhari ya ce, "Ai kam tinda nazo naje na dubo Yaa Aslam da amarya." Shiru Momy tayi kawai. Momy ta ce, "To ni me kake so nai maka ne." "Duk abinda Momy tayi nagode." "To ai shikenan. duk abinda ka gani ka godewa Allah tinda kaki zaba." Dariya Buhari yayi. Momy ta ce, "Kaje ka huta ko?" Kai ya dan sosa ya ce, "Aah tukkuna dai zanje gidan wani aboki na daga nan zani gidan Yaa Aslam," Momy ta ce, "Toh!" Momy ya tambaya address din Aslam sannan ya fice. Yana fita yayi gidan abokin sa anan duk ya bashi katin nan ya rabawa sauran abokan su. Daga nan yayi gidan Aslam. Gida ne mai kyau ya hadu, yana zuwa ya ce, "Oh ikon Allah da tini Asmmy na ce a gidan Yaa Aslam. ikon Allah ance matar mutum kabarin sa ko nan gaba zasuyi aure waya sani sai Allah." Yana parking ya kira number Aslam. Aslam na dagawa ya suka gaisa kamar yadda suka ssaba. Buhari ya ce, "Yaa Aslam gani a compound din gidan ka." Aslam da sauri ya mike ya ce, "Da gaske." Ya ce, "Kazo ka gani." Da sauri ya katse wayar ya fito. Yana ganin Buhari ya rumgume shi. Dariya ya saki ya ce, "Amman naji dadi mu shiga daga ciki." Suka shiga. A falo suka zauna. Aslam shi ya kawo masa ruwa da lemo. Sanna suka zauna hira yana tambayar sa ya Mami da Mutan gidan. Dan sunan Asma'u ma ya kasa ambata. Duk da a cikin ransa yana son ya tambayi Ya Asma'u take amman ya kasa. Buhari ganin bai ga Matar Aslam ba ya , "Yaa Aslam Ina Anty nawa." Kai Aslam ya dan sosa ya ce, "Ta fita unguwa ne." Buhari ne ya mikawa Aslam katin bikin sa. Amsa Aslam yayi yana washe baki yana ta sanya albarka. Har magariba suna tare dan a gidan sukai sallah. Buhari ya tashi zai tafi kenan sai ga Pretty ta shigo. Cikin shigar riga da wando, kayan sun matse ta sai wani mayafi da ta yafa abin ba kyan gani. Buhari da farko bai gane wace ba sai da ya ga Aslam ya ce, "Madam! Barka da zuwa." Kallon su tayi a yatsine ta watsar ba tare da ta ce, Uffan ba ta wuce ta kwanta akan kujera tana kwallawa daya daga cikin yan aikin ta kira. Da sauri ta karaso. Ta bata umarni ta dauko mata lemo. Mikewa tayi da sauri ta miko mata ta dawo. Buhari kuwa ya baki ya saka yana kallon ta. Kallon su tayi a yatsine ta ce, "Ina zaka ne?" Kai Aslam ya girgiza ya ce, "Raka shi zan yi." Tsaki Buhari ya saki yayi waje. Da sauri Aslam ya biyo shi a baya. Yana karasawa ya shiga motar sa. Aslam ne ya leko ya ce, "To bro nagode a gaida gida da su Mami. Sai munzo bikin ko?" Kai Buhari ya daga ya ce, "Allah kawo ku." Yai gaba. A ransa yana mamakin wacce irin mata Aslam ya aura. Anya kuwa haka ta bar shi. Da wannan tunani ya karasa gida. Yana zuwa Momy ya tadda a falo. Abinci ta bashi ya ci sannan suka tsaya hira. Can Buhari ya ce, "Momy daman haka Matar Yaa Aslam take?" Momy ta ce, "Ta maka rashin mutuncin ko?" "Uhmm batai min komai ba. Ni ko kallo na ma batai ba. Amman Momy kinga da shigar ta take yawo. Bayan nasan Yaa Aslam ba yason shigar banza. Kuma Momy sam bata da tarbiyya kinga irin kallon da take mana kuwa." Ajiyar zuciya Momy ta sauke ta ce, "Wallahi kowa complain din da yake min kenan in yaje gidan Aslam. Bansan me yake damun Aslam ba. Amman abin ba dadin ji. Ka ganni nan ban taba ganin ta ba ma bare na san ya take." Kai Buhari ya girgiza ya ce, "Momy bafa kiga ba." Momy ta ce, "Uhmm wallahi Buhari na rasa ya zanyi, ni yadda aka ce min ma ita ta zama mijin ma. dan sai ta ce yayi zai yi in kuwa ta ce, A'ah bazai taba yi ba. Baka ga ba duk ya zama wani iri abin tausayi. Anan fa kullum yake cin abinci dan wata rana ma ni nake aika masa har gida. Wallahi al amarin Aslam yana bani mamaki sosai." Buhari ya ce, "To Momy bakya ganin ba haka suka barshi ba. In ba haka ba, abin ai yayi yawa." Shiru Momy tayi tana nazari ta ce, "Kuma fa haka ne, wallahi ban taba kawo haka ba. To yanzu ya zanyi." Buhari ya ce, "Zan fadawa Mami da Asma'u bama Asma'u tana da sani sosai a addini. Nasan zata san abin yi. Amman dai ya dage da addu'a muma mu dage da taya shi da addu'a." Mami ta ce, "Insha Allah!" Haka suka tashi suka tafi kowa ran sa ba dadi. Buhari kuwa sosai yake tausayawa Aslam dan ya kasa sukuni. A haka yai bacci. Cikin dare ma ta shi yayi ya dinga masa addu'a. Asma'u kuwa Sai magariba ta koma gida. Tana shiga taga motar Sir Sabir. Kai ta dauke tayi cikin gida. Yana zaune a falo yana cin tuwon da Mami ta dafa. Tana shiga suka hada ido. Durkusawa tayi ta gaishe shi ya amsa yana binta da wani kallo wanda tasan Yaa Aslam na mata. Ido ta dauke har zata wuce sai kuma taga Mami ta fito daga kitchen hannun ta rike da lemo da ruwa. Karasawa tayi ta amsa, sannan ta zauna. Mami ce ta kalle tace, "Kun dawo?" Kai Asma'u ta gyada. Mami ta ce, 'Buhari ya kira ki ne?" "A'a! Ya na ina ne banga motar sa ba." Mami ta ce, "Ya tafi Abuja," Wata faduwar gaba taji dan tasan wajen Momy yaje, kuma zai hadu da Yaa Aslam. Shiru kawai tayi ta jingina da kujera tana lumshe ido. Mami ce ta lura da canjawar da tayi. Kallon Sabir tayi shima Asma'un yake kalla. Mikewa Mami tayi ta hau sama. Yana jin shigar war Mami daki ya matso kusa da ita ya zauna. Asma'u bata ji zaman sa ba sai kawai muryar sa da taji a dai dai kunnen ta. Ido ta bude da sauri. Ido suka hada yana kallon ta ido cikin ido. Duk sun kasa dauke idanun su. Shi wani kallo yake aika mata. Ita kuma wani abu taga yana fitowa daga idon sa yana shiga nata. Da sauri ta lumshe ido dan baza ta iya jure kallon da yake mata ba. "Husnah!" Ya kira sunan ta cikin sanyin murya. Ido ta bude a hankali ta sadda kan ta kasa. "Husnah! Wai haka kike so ki cigaba da rayuwa ba farin ciki. Ke kenan baza ki samu wanda zai sa ki farin ciki ba. Ki tattara komai naki kin bawa Yaa Aslam, husnah ba haka rayuwa take ba. A duk sanda wani ya ce baya yi da kai a lokacin wasu keyi dake, ki dauri ki ban dama zan kasance miki yadda kike so na kasance." Shiru Yayi yana kallon ta. Idon ta alumshe kuma daga dukkanin alamu tana jin sa. Kuma maganar ta ratsa ta. "Husnah!" Ya kara ambatar sunan ta. Bude idon ta tayi da sauri jin kamar muryar Yaa Aslam. Sai dai me ba shi bane, mikewa tayi da sauri tayi hanyar bene. Har ta hau sai kuma ta juyo. Kallon sa tayi shima ita yake kalla. Murmushi ta sakar masa kawai ta haye sama. Mamaki ne ya lullube shi. Ya rasa murmushin nata me yake nufi. *MS Indabawa* [1/18, 14:29] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Part *2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da juriya Online writer's* Dedicated to *My lovelly Mum* *31-35* *Ba abinda zzan ce da masoya karanta littafai na sai godiya mai tarin yawa.* *A gaskiya ina alfahari da ku. Allah ubangiji ya bar zumunci. Ina kaunar ku saboda Allah* Zama yayi shima yai murmushin kawai. Mami ce ta sauko. Hira suka dan taba sannan yai masu sallama ya tafi. Zuciyar fal da tunanin Asma'u. Yana kaunar Asma'u son Asma'u yai masa wani irin kamu. Asma'u kuwa tana shiga daki ta fada kan gado. Ido ta lumshe ba wanda ya fado mata sai Yaa Aslam, Ta jima tana juyi duk ranta ba dadi sannan ta mike ta shiga cire kaya. Tana gamawa ta fada bandaki wanka ta fara. Tana gama wa ta tayi alwala. Sai da ta shirya cikin kayan baccin ta dogon wando da riga fare tas sannan ta tada sallah. Ta jima tana addu'a kan Allah ya kawo mata dauki sannan ta Mikewa jiki a sanyaye ta bude firij. Lemo ta dauko ta koma kan gado ta zauna. Wayar ta ta dauka ta latsa number Yaa Buhari. Da sauri ya dauka. Murya ta shagwabe ta ce, "Yaya shine ka manta dani ko?" Murmushi yayi ya ce, "Tayaya zan manta dake Sis. Na ta neman number ki ke da wife ban same ku ba." Ajiyar zuciya ta sauke ta ce, "To Yaya Ya hanya yasu Momy da Dady." "Suna lafiya. Ince kuma kuna lafiya." Kai ta gyada masa. "Asma'u me yake dumun ki?" Dan yaji muryar ta ba dai dai ba. Damuwar ta tai kokarin kawar wa sannan ta danyi murmushin karfin hali ta ce, "Ba komai." "Kin tabbata?" ya tambaye ta. Kai ta gyada masa. Yace "To sai da safe." Sukai sallama. Kwanciyya tayi tana tunanin Sir Sabir kuma. "To tinda na rasa Ya Aslam me yasa ba zan karbi duk wanda ya so ni ba. Sir Sabir bai da makusa. Yana da kyau ga ilimi ga addini ga nutsuwa me kuma zan nema bayan nan." Tayi juyi, ta kuma fadin, "Duk da haka dai ina son Yaa Aslam ko ba komai Yaa Aslam yayanah ne," Hawaye ne ya zubo mata. Ta jima tana kuka sannan ya mike tayo alwala ta tada sallah. Ta jima tana kai kukan ta gun Allah. Sannan ta hau karatun Alkur'ani. Har akai sallah asuba tana kan sallaya. Wanka ta kara yi sannan ta dawo ta tada sallah. Tana idar wa ta fada kan gado sai a lokacin wani bacci mai nauyi ya dauke ta. Mami tinda ta tashi bata ga Asma'u ba ta leko ta tadda tana bacci ta sauka kasa kawai. Dan tasan ba zata aiki ba tinda bata sauko ba. Aiki tayi ta hada musu break sannan ta yi wanka. Har karfe biyu Asma'u bata sauko ba. Mami Ta hau sama ta dubo ta yafi sau uku amman bacci take kuma jikin ta ba zazzabi. Wannan ne yasa Hankalin Mami ya dan kwanta. Karfe biyu da rabi Zainab ta karaso gidan. Mami ta gani zaune a falo. Har kasa ta durkusa ta gaishe ta cikin jin kunya. Mami ta amsa cikin sakin fuska da soyayya. Mami ta ce, "Ki hau sama yau tana can ko aikin ma bata je ba." Zainab ta ce, "Mami lafiya dai ko?" Mami ta ce, "Lafiya lau, ina jin dai abin ne ya fado mata kuma." "Allah sarki." Zainab ta fada tana mikewa. Ta ce, "Mami addu'a dai xamu ta taya ta da ita." "Haka ne, Zainab Addu'a kuma kullum yi muke. Sai dai fatan Allah ya amsa.' "Ameen!" Ta hau sama. Asma'u na kwance ta daka mata duka. Da sauri ta mike tana sosa wajen da ta dake ta. Tana mutsuka ido. Kallon ta Asma'u tayi ta ce, "Zainab har kin zo?" "Eh! Kinsan karfe nawa kuwa?" Ta fada tana kallon idon ta da suka kumbura saboda kuka. Asma'u ta ce, "Uhmm wallahi bacci na sha ban sani ba." Ta fada tana mikewa tsaya, kallo Zainab tabi ta dashi har ta shige bandaki. Kai ya girgiza, a rayuwar ta tana son Asma'u tana jin Asma'u kamar kanwar ta, duk abinda ya damu Asma'u itama damun ta yake. Ta rasa tayaya zata shawo kan Asama'u har ta daina damuwa. Duk da tasan da wuya. Mikewa tayi ta gyara gadon ta share dakin sannan ta koma ta zauna. Tana zama Asma'u ta fito tana tsane jikin ta. Kallon dakin tayi ta kalli Zainab ta ce, "Ke dai bakya gajiya wallahi." Ta zauna tana shafa mai, ta ce, "Yau ina zamu?" "Ke dai ki sauri zamu je, madobi fa." Kai Asma'u ta gyada. Mai kadai ta shafa ko powder bata shafa ba ta mike ta saka wata doguwar rigar Atamfa. Mai A shape. Tana da dogon hannu. Mayafin after dress ta yafa ta dau wayar ta da mukullin mota ta ce, "Muje ko?" Zainab ta ce, "Kin karya ne?" "A'ah muje zan dau Maltina ta ishe ni ma." Mikewa tayi tabi bayan ta. Mami tana falo tana ganin su ta saki murmushi ta ce, "Kun fito." Asma'u ta ce, "Eh! Mami ina kwana?" Mami ta amsa, da "Lafiya lou kin tashi lafiya?" Kai ta gyada ta mike ta nufi firij din falo ta dauki Malt guda biyu ta ce, "Mami mun fita zamu je Madobi wajen yan ajin mu." Mami ta ce, "To a dawo lafiya. Allah kiyaye hanya." Suka fita. Suna fita suka ci karo da Sir Sabir zai shigo. Wajen sa suka karasa suka gaishe shi cikin girmamawa. Amsa yayi yana bin Asma'u da kallo. Bai taba ganin ta da irin wannan shigar ba. Zainab ya kalla ya ce, "Amare ina zaku ne?" Asma'u, Zainab ta kalla ta ce, "Wallahi kati zamuje rabawa daga nan mune har madobi." Kallon su yayi ya ce, "Madobi da kanku. A'ah muje na kai ku. Daman Buhari yai min maganar zuwa Madobin." Asma'u, Zainab ta kalla ta ce, "Sis kinga Sir Sabir ya rage miki aiki." Asma'u dake danna wayan ta, ta dago ta kalli Zainab sannan ta kalli Sir Sabir da ya zuba mata ido. Murmushi ta dan saki ta ce, "Da ka huta ai." Dan Hararar ta yayi ya ce, "Ku shige muje." Ya bude mata gidan gaba. Zainab dai kallon su ta tsaya yi tana cewa Allah yasa Sir Sabir ya so Asma'u dan ba karamin dacewa sukai ba. Ga wani kallo da taga yana binta da shi. Da haka ta shiga gidan gaba. Zainab ta shiga cikin gidan baya. Maltina ta mikawa Zainab sannan ta mikawa Sir Dabir dayar ta hannun ta. Bai amsa ba ya ce, "Ke fa?" Murmushi tayi ta ce, "Na koshi." Ya ce, "Ban yadda ba sha ki rage min." Zata ce A'ah ya ce, "Ki sha ki ragen in ba rowa zaki min ba." Fasawa tayi ta sha kadan ta mika masa, hannu ya kawo zai amsa ya hade da hannun ta. Kallon sa tayi ya kashe mata ido daya. Kai ta dauke ta cigaba da kallon titi. Shiru tayi sai Zainab da Sir Sabir da suke hira. Sai dai shi da yake dan tabo ta, in anyi abu ya ce, "Ko Husnah?" Da haka har suka karasa gidan su Hafsat. Anan suka dan jima dan shima Sir sabir suna tare da Baban Hafsat. Har abinci suka ci sannan suka taho, ranar shi ya dinga yawo dasu daga can zuwa can. Har magariba sannan ya kai Zainab gida. Ana sukai sallah magariba sannan Asma'u tai mata bankwana suka taho. A mota kuwa kowa shiru yayi shi yana tunanin taya zai kara cusa kan sa awajen Asma'u dan ya tabbata Asma'u baza ta ki shi ba sai dan kawai tana son Yaa Aslam ne. Itama a zuciyar ta rokan Allah take Allah yasa kar yai mata maganar dan bata so. Can ya dago ya kalle ta ya ce, "Kin fadawa Maryam bikin ne?" Kallon sa ta danyi sannan ta kawar da kai ta ce, "Na fada mata, ta ce, next week ma zata zo." Kai ya gyada ya ce, "Oh yanzu dai kun zama friends ko? Murmushi ta dai yi kawai ba tare da ta bashi amsa ba. Ya ce, "Yaushe za muje ki gaida Mamah?" "Ko yaushe ma!" Ta bashi amsa. "Da gaske?" Ya tambaye ta. Kai ta gyada. Kallon ta yayi ya ce, "Ko yanzu ne?" Kallon jikin ta tayi ta ce, "A'ah dai." "Saboda me?" Ya tambaya. "Kalli jiki na fa?" Ta fada tana kallon kan ta. Murmushi yayi ya ce, "Me jikin naki yayi?" "A'ah dai." Ta fada tana tsare shi da idanun ta. Da yake shima ita yake kalli take yaji motar na neman kwace masa. Saboda idon ta da suka ruda shi. Da kyar ya kamo motar ya cigaba da tukin. Daga haka bai kara cewa komai ba, har suka kara sa gdn. MS Indabawa [1/18, 14:30] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR*  ASMA'U HUSNAH BY *MARYAM S INDABAWA* *MANS* 🌐 *HAJWO* 🌐 *Hakuri da juriya Online writers*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 *Gidan Hakuri da juriya tare da kawar da kai, gidan zaman lafiya. Na gaida ku.* *36-40* Dedicated to My great *Mamah* Allah ya jikan ki ba dan kin mutu ba. Allah kara miki lafiya da nisan kwana mai albarka. Nagaida ke mahaifiya ta abar alfahari na. *Manzon Allah (SAW) ya ce, Idan zaka so mutum kada ka nuna masa tsananin so. in zaka kisa kada ka nuna masa tsananin ki. Dukkan su hankalin su ne yayi kan motar, banda *Asma'u* da ta daukar da kan ta, tana wasa da wayar ta. Khadija ce ta fara magana, ta ce, "Kai motar nan ta hadu amman." Amina tace, "Ai daga duk kan alamu, ma na cikin ta zai fi haka hauduwa." "Gaskiya kan motar ba karya, ko wane dan gayun ne a ciki." Hafsat ta fada "Ni kam ba ruwana da na ciki sai motar da ta burge ni." Zainab ta fada. "Kai Allah bani irin motar na." Hafsat ta fada. "Hassada kike yi tinda kika ce Allah baki irin ta sai dai kice Allah baki finta." Amina ta fada. "Duk karya ne irin haka nan, dan kaga Abu ka roki Allah yabaka irin sa shine haka." Zainab ta fada tana tabo *Asma'u* " *Asmy* kalli waccen motar amman tayi kyau wallahi." Kai ta dago ta kalli motar, ji tayi gaban ta ya fadi. "Eh tayi kyau." Ta fada tana mikewa sakamakon kiranta da ake yi. Can gefe ta koma jikin wata motar, ta dauki wayar. "Hallo my beauty! (Kyakyawa)" "Ya Aslam wannan ai tsokana ce." amsa ta amsa masa da muryar shagwaba. "Wacce tsokana nayi." ya tambaya "Wai beauty!" ta bashi amsa. "Oo Ke ba kyakyawar bace." Ya tambaya. Ta ce, "Gaskiya ni ba kyakyawa bace. Wannan ai sai kasa ayi min dariya." "Ba wanda zai miki dariya kinji, saboda kyan ki ba kowa ke da irin shi ba. Kina da wani kyau wanda kafin a samu mutum me irin sa ake dade wa. Ur skin is fresh with a beauty colour. (Fatar ki a murje, me kala me kyau)." Ta ce, "Uhmm please stop dis joking I beg you. (Dan Allah daina wannan tsokanar na roke ka." Murmushi yayi ya ce, "Wallahi I am not joking, I am telling the true. (Ba tsokanar ki nake ba ina fadan gaskiya ta ne.)" Baki ta turo ta ce, "Naji ya isa, ka karaso ne," "Eh! Gani kina ina ne." Ta ce, "Ina kofar department din mu," "Nima ina wajen." "Kai ya Aslam!" ta fada. "Da gaske ina wajen." "Ta ina." "Ina cikin wata Ash marsandi." "Oh na ganka. Ina ta bayan ka." "To kizo man." "A'ah Yaya please kai ka fito." "To gani nan." Baya ta juya masa. Kofar motar ya bude, wani sanyi da kamshi me dadi ne ya fito. Kafar sa ya ziro kasa. Safa ce da takalmi sau ciki bakake a kafar sa. Daya ya diro sannan ya fito gaba dayan sa. Suit ce a jikin sa, ruwan kumkumadi. Ya cire ta saman sai yar ciki da ya rage. Tin daga kafar sa na fara kallon sa inayin sama. har na karasa kirjin sa wanda yake a bude dashi na kirar cikaken namiji me jini a jiki wanda ya cika namiji. Kan fuskar sa na gangara. Fuskar sa me kyau ce doguwa fari ne tas dashi, sai manyan idanu wadan da suke a lumshe, wanda ake ce musu (sexy eye) Bakin shi dan karami ne, wanda yake da lebe me taushi gasu pink sai kwalli suke. Kansa cike yake da suma, kamar ta indiyawa. Sai saje dake gefen fuskar sa, wanda ya kara fito masa da kyaun fuskar sa. Idon sa sanye da farin gilashi. Masha Allah wannan gayen duk inda ake neman cikaken namiji me kyau da kwarjini ya kai ya ma wuce nan. Yan mata da yawa kallon sa suka tsaya yi sai gulmar sa akeyi. Dan ya gama haduwa ba karya. Waige waige ya farayi dan neman inda take, duk da ta juyar da kanta sai da ya gene ita ce. Dan duk jikin sa ya gama shaida masa, *Husnah* sa ce. Cikin tafiyar kasaita da nuna kalama tare da nutsuwa yake tafiya. Sannu a hankali har ya karasa gefen ta. Ta bayan ta ya zaro hannayen sa dake cikin alhiju ya rufe mata idanu. Jin an rufe mata ido da hannu me laushi, ga kamshin turare dake tashi, tasan Ya Aslam ne. Murmushi ta saki me sauti. "Haba My Hero, ai nasan kai ne." Hannun sa ya janye ya maidasu kan kafadun ta ya juyo da ita. Kasa magana yayi ya kure ta da idanu. Ido ta kashe masa guda daya. "Yah dai." Yawu ya hadiye tare da sauke ajiyar zuciya yana me sakin wani murmushi dake karawa fuskar sa kyau. Wani kallon soyayya yake aika mata dashi. Ba karamin kyau sukayi ba. "Baby nah kinyi kyau fa." ya fada yana kara kallon ta. "Zaka fara ko?" Ta fada tana nuna masa wasu kujeru da aka gina su. Zama yayi ita ma ta zauna. "Sannu Yaya nah Ya hanya?" ta tambaya cikin kulawa. Ya ce, "Hanya Alhamdulilah." "Sannu toh!" "Yauwah! Naji dadin zuwa na dana ganki Sweetheart, kin kara kyau, ashe duk hoton da nake gani rage min kyaun ki yake yi." "Yayana kenan yasu Momy." ta fada tana wasa da yatsun hannun ta. "Suna lafiya." Ya fada yaba dago face din ta. "Bari na karbo maka lemo." Ta mike. Kamo hannun ta yayi ya ce, "A'ah yanzu na gama cin abinci ga naku can ma a mota." Murmushi tayi, "Kai Yayah." "Eh!" "Zakaje gida ne." "A'ah! Daga nan zanyi gida." "Ok." "Ina sonki Baby nah." Murmushi tayi ta dukar da kanta. "Baby kunyar nan taki tana dada miki kyau." Kai ta kuma dukar wa. "Bari na wuce kar nayi dare. Tinda naga Baby nah ai nagodewa Allah." Murmushi tayi. "To nagode." "Nike da godiya Baby nah " Suka mike suka nufi motar. Dai dai karasowar Sir Sabir zai dauki motar sa. Kallon juna suka yi, ya shige motar sa. "Waye wancan." Juyawa tayi, "Sir Sabir wani lecturern mune." "Kuna magana ne?" Ya tambaya fuska a dan hade Kai ta girgiza ta ce, "A'ah!" "Ina zee kuwa?" Ya tambaya. Kallon gun da suke tayi ta ce, "Gata can bari na kira ta." Ta tafi wajen su Zee, "Zee kizo inji Ya Aslam!" Ta fada tana kamo hannun ta. Wajen su suka karasa. "A bamu waje ko?" Ya fada yana kallon *Asma'u* baki ta tabe ta bar wajen. Dariya yayi, yace, " *Husnah* rigima." Sannan ya dawo da hankalin sa kan Zee. Bayan sun gaisa yake bata amanar *Asma'u* sannan sukayi sallama. Wajen *Asma'u* yayi, "Haba Baby na yanzu da Yayan naki kike fushi. Kiyi hakuri kinji." Shiru tayi masa. Murmushi yayi, ya koma gaban ta, "Ko so kike na rumgume ki na rarashe ki." Ido ta zaro, tana girgiza kai. Ya jawo ta. Saurin janye hannu ta tayi. Tayi wajen motar sa. Bayan ta ya bi, yana Murmushi ya shiga motar. Leda ya miko mata. "Gashi ni zan tafi." Amsa tayi ta ce, "To Allah kiyaye hanya." "Ameen nagode!" Ta rufe masa kofar tana daga masa hannu. Tare da murmushi akan fuskar ta. Sai da taga bata hango shi sannan ta koma wajen kawayen ta. Ido suka bita dashi, " *Asma'u* waye wancan." Hafsat ta tambaya fuskar ta a hade. Kallon ta *Asma'u* tayi sannan ta dauke kai. Zainab ce, tace, "Yayan ta ne." Khadija tace, "Amman fa ya hadu. Wai meyasa ke kike baka ne." Amina ce, tace, "To ko zaki canja mata halitar ta ne," Harara ta Khadija tayi, "Ni na tambaye ta, ta wani haden rai da dauke kai." Hafsat ta fada, Mikewa *Asma'u* tayi ta kalle ta. "kin tambayen an amsa miki ba shikenan ba. ko kin manta wa kike tambaya ne. *Asma'u* da batai miki komai bace kika dau gabar duniya kika daura mata, kin manta in nayi miki magana ko kallo na bakya yi shine kuma yanzu zaki zo kina tambaya ta. Kuma cikin isa sai kace ni yar kice. Ke bama zan fada ba. Kiyi abinda xakiyi." Ta fada tana kama hannu Zainab suka shige hall. "Haba *Asma'u* me kenan kika yi ke da bakya fada." Kuka *Asma'u* ta fashe dashi, "Ya zanyi kema kinsan dai Hafsat ta kaini bango ne. Duk makarantan nan ba wacce ta tsana kamar ni tin ina dauke kai sannan yanzu tazo tana min gadara. Akan abinda be kai ya kawo ba." "Ya isah toh mene na kukan!" Ta fada tana jan ta jikin ta tana rarashin ta. Ta jima tana addu'a cikin ranta sannan taji sanyi. Kan ta, ta dago ta kalli Zainab. "Nagode besty." "Ba komai." kasa ta duka zata dauki jakar ta. Sai a lokacin ta tuna da abinda Ya Aslam ya kawo musu. Murmushi tayi ta dauki ledar tana dubawa. Takeaway yayi musu, guda uku sai dayar ledar kuma kaji ne guda biyu a ciki da lemuka na jarka. Raba su tayi gida biyu ta mikawa Zainab. "Besty dan Allah mikawa su Amina kayan nan." Karba tayi tayi waje. Su *Asma"u* na barin wajen, su Amina suka farayiwa Hafsat fada. "Haba Hafsat, meyasa kike haka, yarinya bata tsare miki komai ba amman kin tsane ta gaskiya ki daina haka." Hafsa ta ce, "Tayaya zakice bata taren komai ba, yarinyar da ta shigo ta same ni sannan tazo tafi ni kokari shine bata fini komai ba." Khadija ta ce, "Yo dan tafiki kokari, ai kema dagewa ya kamata kiyi ba ki tsane ta ba." Khadija ta fada tana bata fuska. "To ku dake ni mana." Hafsat ta fada. "A'ah A'ah ba abin duka anan. Sai dai muyi miki addu'a Allah ganar dake." Dai dai nan wata daliba da tayi kaurin suna a makarantar ta karaso gun su "Hae Babies." "Hae!" Gefen Hafsat ta zauna. "Dan Allah wa naga ta tsaya da yaron nan da yazo yanzu. Dan bayan ta na gani banga gaban ta ba." "Oh ai *Asma'u* Suleiman ce." Hafsat ta bata amsa. "Wane department take," Suka fada mata tai musu godiya ta bar wajen Zainab na fitowa Munasha na shiga Hall wajen *Asma'u* ta dosa kai tsaye, Toh masoya *Asma'u Husnah* naga sakon ku na gode, ba ma yan threestart u always love my story tnc Allah bar kauna. Hhhh yan facebook comment naku na min dadi ngd Afternoon yan uwa Don't forget to vote pls *INDABAWA* [1/18, 14:30] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Part *2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da juriya Online writer's* Dedicated to *My lovelly Mum* Pagr *41-45* Yau Yaa Buhari yana tashi ya fara shirin tafiya. Mami taso ya kara kwana ki to amman ba lokaci, dole haka ta bashi sakon Asma'u. Kaya masu yawa ta aiko mata sannan ta bata sakon tayi amfani da kayan laifen da aka hada mata. Sunyi bakwana kan cewa nan da kwana biyar zata taho Kano ita ma. Haka Yaa Buhari ya taho yana kewar ta, a ransa kuma yana sa ran sai komai ya gyaru dangane da Yaa Aslam. Asma'u kuwa washe gari ta tashi lafiya sai dai damuwa dake damun ta sosai. Da farko akwai damuwar ta, ta rasa masoyin ta sai kuma damuwar, da Sir Sabir, yake ciki. Tasan matsalar so tasan halin da ake fadawa na rashin samun masoyi. Dan haka dole ta tausayawa Sir Sabir. Ta sa a ranta zata aminta da Sir Sabir ko da bata son sane. Da wannan shawar da ta yanke kuma ta tuna wane Sir Sabir wajen kyawun hali yasa ta dan ji dama dama a zuciyar ta. Dan har waya sukai da Maryam ta ce, mata tare zasu zo da kawar ta Nusaiba. Asma'u kam murna har tana cewa su taho cikin satin nan. Sannan ta ce, ta aiko da measurement din su za'a kai dinki. Sosai Maryam tai murna ta ce, mata insha Allah ran juma'a zasu zo kafin sati biki kenan. Suna gama Waya Mami ta sauko ta ce, "Asma'u dawa kike waya ne haka?" Asma'u ta ce, "Mami da Maryam 'yar yar Sir Sabir muke waya ranar juma'a ma zasu zo biki." Mami ta ce, "To fa. Allah dai ya nuna mana bikin nan lafiya." Asma'u ta amsa da "Ameen!" Mikewa tayi ta shiga kitchen ranar ita ta shirya musu abincin rana. Sannan ta shiga tai wanka ta ce, zata je ta kai musu dinkin dan har da Hafsat da Maimuna za akai dinkin. Mami ta bata kudin dinkin isashe ta fita. Zainab ta biya ta dauka sannan suka wuce Zoo road inda zasu kai dinkin. Kayan ta bashi ta ce, zata turo masa da measurement din su ta waya. Ta bashi kudin dinki suka wuce wajen da Yaa Buhari ya bada a bugo musu littafi da jaka da calender. Har ya gama suka amsa suka nufi gida. Ya Buhari sai Yamma ya dawo lokacin Asma'u bata gida. Wanka yayi ya bawa Mami sakon ta sannan ya fice yai wajen Sabir. Asma'u kuwa, suna dawowa ta kai Zainab gida tayo gida a gajiye. Sabani suka samu da Yaa Buhari dan tana tafiya shi kuma ya nufi gidan su Zainab. Asma'u na shiga taga motar Yaa Buhari cikin gida ta shiga da sauri tana kwala masa kira. Mami dake falo ta ce, "Oh Asma'u!" Dariya Asma'u tayi ta ce, "Mami ina Yaa Buhari nane?" Mami ta ce, "To ya fita kije ki wanka, kizo ga kaya can Momy ta aiko miki." Mikewa Asma'u tayi ta ce "A'ah Mami kayan zan fara gani tukkunna." Tayi sama da sauri. Dakin ta ta shiga akwati ta gani babba ta bude. Kaya ne masu kyau da tsada wanda Momy ta saba aiko mata dasu duk karshen wa. Amman wannan kyan nasu yafi karfin wasa. Kayan dai fitar biki ne, sai wata shadda da ta gani a dinke kala biyu da ta tata da ta Mami. Da wani material shima iri daya amman dayan pink dayan kuma green. Mai pink dine nata green din na Mmai. Har da takalma da jaka duk da fashion dankunne da sarka. Sosai taji dadin kayan duk da dinki nan da tayi. Cikin akwatin ta mayar ta rufe ta zauna ta zuba tagumi, Murmushi ta danyi ya ce, "Allah sarki da yanzu muna tare da Momy. To Allah bai ba. Allah yasa haka ne mafi alheri." Ta mike tana maida kwalar da ta fito mata. Dady ne kuma ya fado mata. Wanka ta shiga tana yi tana zubar da hawaye. Har ta gama ta fito, ta shirya sannan ta gaye gado. Dan bata da walwalar da zata iya sauka kasa dan kar ta dagawa Mami hankali. Tana kwancen nan take zancen zuci ta ce, "Ni kam wai haka rayuwa ta xata kare kenan ban da walwala banda farin ciki. In kuwa har haka ne, zancen Sir Sabir zai faru na, zan iya kamuwa da wani ciwon bayan kuma ina da masoyan da zasu damu dani." Juyi tayi ta rufe idon ta duk dan ta samu tayi bacci. Asma'u sai karfe tara na dare ta mike, sallah tayi ta kara komawa gado ta cigaba da bacci. Washe gari tana tashi ta shirya cikin Wata bakar abaya wacce akai mata aiki da golding zare. Sandal ta saka golding da jaka golding tai rolling kanta da bakin mayafin rigar. Ba karamin kyau tayi ba duk da ba kwalliya tayi ba. Sai kamshi take tashi. Dakin Yaa Buhari ta shiga ta tada shi yana bacci, fita tayi ta sauka kasa. Mami na kitchen ta karasa ta gaida ta, sannan tai mata sai ta dawo. Fita tayi ta dauki motar ta ta nufi wajen aiki, tinda taje take kwance ta kasa komai. Tana kwance Sir Sabir ya shigo. cikin shigar sa ya saka bakar suit yayi kyau da shi. Fuskar sa sai annuri take fitar wa da wani murmushi mai sanyayya zuciyar wanda akai dan shi. Jin shigowar sa yasa ta Mike da sauri, kallon sa ta yi, tai kasa da kai ta ce, "Ina kwana?" Zama yayi a gefen ta, yana kallon ta kafin ya amsa da "Lafiya ya kike?" "Lafiya lou!" Ta bashi amsa. Shiru sukai, Jin shirun yai yawa yasa, ta jingina kan ta a akan kujerar da take zaune. Ido ta lumshe kamar me bacci. Kallon ta Sir Sabir yayi. Ta kara kyau da ita. Ajiyar zuciya ya sauke, sannan ya ce, "Bakya jin dadi ne?" Kai ta girgiza cikin sanyin jiki tai masa murmushi ta ce, "Lafiya kalou nake, kawai garin ne?" "Garin ne?" ya tambaye ta. Kai ta gyada masa, murmushi yayi ya ce, "Taso mu fita to!" Mikewa tayi dan baza ta iyai masa musu ba. Fita sukai suka dinga zagaye gari shine kai ta can shine kai ta can. Duk wajen da yasan zai ta ji nishadi ya dinga kai ta. Har la'asar suna yawo a gari. Abinda yake buri ya samu. Dan sosai ta sake har hira suke. Daga nan ya dauke hanyar yayi hanyar gidan su. Sai da suka shiga sannna ta kalle shi ta ce, "Ina ne nan?" Ido ya kanne mata ya ce, "Gidan mune!" Kallon sa tayi tai kasa da kai. Fita yayi ya bude mata. Fita tayi tabi bayan sa. Gida ne mai kyau gashi kato. Ciki suka shiga da sallama. Mamah na zaune kan kujera, tana kallon suka shiga. Suna shiga Mamah ta mike tana cewa, "A'ah wa nake gani.kamar Asma'u!" Ta kamo ta. Sabir ne ya ce, "Ba kama ba ce ita ce." A kan kujera ta zaunar da ita Asma'u ta zame ta zauna a kasa. Gaishe da Mamah tayi cikin girmamawa da kunya. Mamah ta amsa cikin sakin fuska tana tambayar ta, yasu mami da Buhari. Ta bata amsa. Mamah da kanta ta kama Asma'u suka nufi daining tana fadin "ince daga aiki kike zo muje kici abinci " Sabir kallo yabi su dashi, ba karamin burge shi sukai ba. Bayan su yabi ya cewa, "Mamah ta samu Asma'u yau ta manta dani." Dariya Mamah tayi ta ce, "Ai dole na kula da Asma'u na manta da kai." Suka zauna. Abinci ta zubawa Asma'u. Shinkafa ce da taloya da miya da taji naman kaji, sai hadin kabeji da lemon kwakwa. Kasa ci Asma'u tayk sai juya cokali da take, sai da Mami ta mike, sannan ta fara ci a hankali. Sabir kam ido ya zuba mata yadda take cin abincin ma daban ne. Jin ido akan ta yasa ta dago. Ido hudu sukai, Cokalin ta ajiye ta daina cin abunci. Da ido da hannu ya tambaye ta 'lafiya' Kai ta dauke kawai, murmushi yayi ya ce, "To sorry Baby nah, kici na daina kallon ki" Ya fada yana dauke ido daga kallon ta, abincin shi yaja gaban sa yana ci. Itama ci ta cigaba dayi. Sai da suka gama sannan suka koma falo. A gidan sukai sallah magariba sannan suka mike tanawa Mamah sallama. Wani hadin turaruka Mamah ta bata, amsa Asma'u tayi tana godiya. Gida suka tafi tare suka shiga ciki. Mami na ganin su ta ce, "To kuna tare kenan!" Kai Asma'u ta daga ta ce, "Kinga kayan da Mamahn Sir Sabir ta bani." Amsa Mami tayi ta duba tana godiya ta kalli Sabir ta ce, "Angode Allah saka da alheri." Murmushi kawai Sabir yayi ya zauna. Asma'u dake gefen Mami ta kalle ta, ta ce, "Mami ina Yaa Buhari?" Mami ta ce, "Yana gun Zainab!" Baki Asma'u ta tabe ta ce, "Yaya ba a kara sauran kwana nawa ta koma gunsa gaba daya." Murmushi Mami tayi ta ce, "Asma'u daru." Mikewa tayi tai sama tana cewa, "Bari naje nai wanka. Nai sallah." Tayi sama. *MS Indabawa* [1/18, 14:32] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR*  ASMA'U HUSNAH BY *MARYAM S INDABAWA* *MANS* 🌐 *HAJWO* 🌐 *Hakuri da juriya Online writers*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 *46-50* Dedicated to my love mother. *Momy nah* Really love u An Ruwaito Cikin Littafin Ibn Sinni, Daga *Anas (ra)* Lallai *Manzon Allah(ﷺ)* Yace: "Shin 'Dayanku Zai Gajiya Ya Zamo Kamar Abi-Damdama?" Sai Sahabbai Sukace Wanene Abu-Damdama Ya Annabin Allah? Sai Yace: Ya Kasance Idan Ya Wayi Gari Yana Cewa: *{Allãhumma Inni Qad Wahabtu Nafsi Wa Irdi Laka, Falã Yashtumu Man Shatamahu, Wala Yazlimu Man Zalamahu, Wwala Yadribu Man Darabahu}* *KARASHEN LBRN Munasha* A cikin kawayen ta mutum daya ce ta arxiki. Wacce tun fara bin mazan ta take mata fada akan irin samarin da take kulawa. Dan ke daga ganin samarin ma xaka san yan iska ne, bare in suna mu'amala suyi ta taba ta. Ko ace za'a tafa. Ko in tana bukatar abu sai dai tace saurayi yayi mata. Rashida yar gidan masu hali ce, dan sau tari takan bata kudi kashe wa. Sannan in an mata kaya kala uku zata dau daya ta bata. Amman sam Maimuna bata godewa Allah. Ita burin ta tagan ta ta kula me kudi wanda zai na kashe mata kudi. Bayan yawancin samarin yanzu basa yin abu dan Allah sai dai in zasu fansha. Rashida takan mata fada. "Haba Maimuna, yanzu da hankalin ki, kike kula wadan nan mazan. Shin me yan mata memukeso muzamane, ina hankalin mu yake ina tunanin muyake ne, Shin iyayen mu me suka gaza yimana muke nema mudorawa kan mu akan hanyar da baza ta bulle da mu bane. Duk kokarin da Baba yake, amman kike son daurawa saurayi duk buqatar ki. Haba yar uwata ashe kinyadda saurayinki xemiki abunda iyayenki baxasu yimiki, Maimuna ki nemo hankalinki da nutsuwar ki6oye son abun duniyarki badon komaiba sedan kitsira da martabarki taki ta 'ya mace. saurayi nagaskiya shine wanda yake sonki da aure baya neman komai daga gareki burinsa yaga kin tsira da mutuncinki. Saurayi mayaudari shine Wanda yake miki hidima ba don Allah ba sedan kibashi gishiri yabaki manda. Mace wadda akasanta da kunya, tarbiyya, mutunci, Jan aji, kamala, sanin yakamata, amman kin manta dacewa yanxu xamani yasanja wasu daga cikin samari sundena abu dan Allah sedan samun riba. wallahi Maimuna, idan saurayi yafuskanci ke kinada kwadayi akwai matsala ta hanyar haka xesamu damar isar da qudurinsa, wallhi saurayi bashida abun duniyar daxe rudeki yaxubar miki da mutuncinki bashida abunda xemiki wanda iyayenki xasukasa. Alokacin bakida damar hanashi duk abinda yanema domin shi kika fara mora. kinsan ko farce yata6a miki yacuceki dan Allah Mainuna ki kula." Duk lokacin da Rashida tai mata fada takan dauka. Amman da ta hadu da yan harkar ta zata manta. In kuma Rashida tai musu fada gaba dayan su, sai suce dan ita Rashida din yar masu Hali ce shi yasa bata san halin da suke ciki ba. Tin asali Yayan Rashida ke son Maimuna, amman tafiyar sa karatu malesia, shi ya sa soyayar ta ja baya. Duk da a cikin zuciyar sa bai da burin da ya wuce ya kamala karatu ya dawo ya tai maki rayuwar Maimuna da mahaifin ta ba. Itama a zuciyar ta shi take so, dan Nasir namiji ne wanda ya amsa sunan namiji, ya hada komai kyau ilimi da gayu. tinda ya tafi be dawo ba duk da suna waya amman karatu yana dauke hankalin sa. Ba dan baya son ta yafi bawa karatu lokacin sa ba. A'ah sai dan son da yake yaga ya kammala karatun sa ya fito da sakamako me kyau. Maimuna kyakyawa ce ajin karshe, fara me kyaun sura. Amman duk ta zubar da mutuncin ta. Har Kungiya ce, da ita wace take daukar yara ta kaisu wajen manyan Alhazai. Wanda har a cikin makaranta ma, akwai wadan da suka daure mata gindi. Yanzu haka Munasha ta zama kwarariya dan ta kama naira a hannu. Yanzu haka da taga saurayi yayi mata zata san yadda zatayi ta ja hankalin sa. Har wajen malamai take kai mutum a janyo mata hankalin sa. Munasha babbar yar duniya ce wcce idon ta ya gama budewa. Ba kasar da bata fita. A harkar karuwanci dai ta fita zakkah. Amman duk da haka, son Nasir na cikin ranta. *-*-*-*-*-*-*-*-* Kwance take a kan gadon ta, sanye take da hijab fuskar ta, tayi kyau da ita. Sai futar da annuri take, allon wayar take kallo. Wannan yasa na mika kai dan ganin abinda take yi. Aslam na gano kwance akan katon gadon sa, yana sanye da blue (ruwan omo) din T-shirt, da blue din wando, da alamar kayan bacci ne a jikin sa. Magana ya ke fada mata kunne na kasa ina sauraro. "Ke na bawa zuciyata *Asma'u*, ki adanata dan nasan zaki mata gata," Murmushi *Asma'u* keyi. Sanna tace, "Hmm Ya Aslam. Gakiya kam zan kula maka da ita fiye da yadda zan kula da tawa." "Nima na sani. na baki ita ne saboda bana son kowa ya taba ta. Duk wanda zai shiga ke zaki bashi izinin shigar ta" Murmushi tayi. Ya cigaba da magana "Dake na fiso muyi soyayya, sannan dake nafi son muyi rayuwa. Dan Banda kamar ki a duniya, wannan yasa na mallaka miki zuciya ta" "Kai Ya Aslam!" Ido ya kanne mata ya ce, "Ke ta daban ce. Shi yasa kullum yabon ki nake. Ke nake son ki kasance a kusa dani. Dan kece kadai farin ciki na." Shiru *Asma'u* tayi tana sauraron sa, tare da lumshe idanun ta. Kallon kyakyawar fuskar ta yake yi. "Ke ce Taurruwa ta. ke kika hasken zuciyata. Kin kawar min da dukkan damuwa ta. Ban da bakin magana gare ki ban san irin godiya da zan miki ba. Ban san kuma me kike son na miki ba." Idon ta, *Asma'u* ta bude, ta kira sunan sa. "Ya Aslam!" Kallon ta yayi kafin ya amsa da "Na'am Baby nah!" Ta ce, "Alkawari nake son karike min koman wuya kar mu rabu kaji." Murmushi yayi, ya gyara kwanciyar sa. Yana kara fuskan tar ta. "Alkawari na rike miki kuma koman wuya bazan rabu dake ba kinji." "Nagode!" Kallon ta yayi yana kashe mata idanu kamar me jin bacci. Kasa tayi da kanta. "Wallahi rabuwar mu abu ce me wuya dan mun zama hanta da jini. Ko 'da da uwa." Dariya ta saka tana girgiza kanta. Shima dariyar yake. "Wallahi da gaske nake. Na fada miki duk abinda kika ji na fada daga zuciyata yake. Abinda zuciya ta take ji kenan baki na ya furta miki." "Na yadda da kai Yayanah. a zuciya ban da kamar ka komai nawa ya zama naka. Amman dan Allah kar ka yadani ka kula da soyayya ta. Dan kai dai na aminta dakai kuma na yadda da kai. Mun shaku mun saba Ya Aslam abin da ya rage kawai auren mu ne." Ta fada yana rufe fuskar ta da tafukan hannayen ta. "Oo please kicire kunyar nan cigaba da narka min zuciya mana." Ido ta zaro "tayaya zan cigaba da narka maka zuciya. Yanzu ya zanyi in na narka maka zuciya." "Sai muyi amfani da taki ko?" "A'ah muyi amfani da taka dai." "To cigaba ina jinki." "Kai Ya Aslam" Kunnen sa ya kama yace, "Yana jira zai kaiwa zuciyar ki abinci taci." Dariya ta saki. "Ya Aslam kenan!" "Allah yunwa take ji fa." "Toh Zan kasance me share maka hawaye a duk lokacin da zasu zuba zan hana su zuba. Zan kyautata maka in faran ta maka." "Allah tabbatar mana da Alheri, sannan nikai na bazan taba barin ki kiyi kuka ba." "Nagode!" "Ba godiya a tsakanin mu." Murmushi sukayi gaba dayan su. "Tashi kije kiyi Alwala kizo kiyi addu'ar bacci." "Toh!" Ta fada tana tashi. Ban daki taje tayo alwala. Addu'a tayi, yana jin ta har ta gama. Wayar ya kashe, sannan ya kirata. Kamar yadda ya saba yi mata kissa Annabawa haka ya farayo mata har bacci ya dauke ta. Washe gari ya kama asabar dan haka tin da ta tashi da asuba tayi sallah. Ta fara gyara dakin ta, tin daga karkashin gado har su durowar ta duk da ba datti amman sai da ta gyare ta goge ko ina. Sannan ta fita madafin su (kitchen) ba kowa a ciki wannan ya tabbatar mata da Mami na can gyaran daki. Dan duk karshen sati sai sun gyare gida ko ina da ina tsab. Wake ta auna tayi waje dashi. Ban garen masu aiki tayi. Baba Lami ta sama zaune. Gaishe ta tayi, sannan ta tambaya ko Lubabatu na nan. Kiran ta Baba Lami tayi. Lubabatu na ganin *Asam'u* ta saki murmushi. "Ina kwana?" "Lafiya lou." "Dan Allah daman waken nan zaki surfa min saboda kar na makara zan je isilamiyya." "Bakomai kawo." Ta mika mata. Ta juya ta fita. Kunun gyada ta dama musu, sannan ta hau gyaran kitchen din nasu. Sai da tagama gyara sannan Lubabatu ta kawo mata markaden. Kayan hadi ta zuba sannan ta fara soya kosai. Kosan kuwa yayi kyau dashi ya tashi abin sha'awa. Tana gamawa ta gyara falon su, sannan ta jere kayan karin nasu a inda suke cin abinci. Kitchen din ta gyara ta wanke duk abinda ta bata. Dakin ta ta koma tayi wanka sannan ta shirya cikin riga da siket yan kanti. Sai ruwan tokar hijab da ta dau wanda yake a wanke a goge dashi. Dakin Dady tayi, ta gaishe dashi sannan suka sauko kasa, Mami ce ta sauko da Ya Buhari, suka gaisa. Sannan suka fara karya wa. Suna gamawa ta mike ta haye sama. Hijab din ta! Ta saka wanda yake har kasa. Sai nikaf da ta saka kafar ta da safa. Jakar ta ta dauka, ta fito. "Mami da Dady na tafi sai na dawo." "To a dawo lafiya Allah bada sa'a" "Ameen!" Ta fice. Yan uwa ya daren? Toh sai Allah ya kaimi gobe in muna da rai da lafiya. Nagode *INDABAWA*: [1/18, 14:33] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Part *2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da juriya Online writer's* Dedicated to *My lovelly Mum* *51-55* don't Forget to vote Da dare akai dinner inda yan mata sukai ankon wani pink material. Amarya kuma ta saka golding kala, ango ma golding shadda ya saka. Asama'u kuma ta saka Dark blue din material sosai tayi kyau. Sir Sabir ma Blue shadda ya saka sai ya fito shima kamar angon Asma'u. Anci ansha an yi liki, duk wanda yaga Asma'u sai ta burge shi dan komai nata da banne ga kyau ga jikin yana dauka. Samarin wajen sun yaba da ita. Sir Sabir kuwa sai kareta yake. Sai da sukaje suna liki ne, kuma sai kuka taga ga Mami ga Yaa Buhari gata ammn ba Dady. Sosai ta sa mutane da yawa kuka a wajen. Anyi taro lafiya an tashi lafiya. Inda washe gari aka dau amarya aka kai ta gidan mijin ta dake rijiyar zaki. Gida ne katon gaske dan Dady ne ya gina masa shi. haka nan an zubawa Zainab kaya sosai. Sai da angwaye suka je sanna suka taho Asma'u na zolayar Zainab Gida su Asma'u suka tafi da su Maimuna da Maryam. Aka bar amarya da ango su kadai a gida. A gida ma wasu dayawa duk sun tafi dan daga Momy sai matar Uncle Abubakar da Uncle iliyasu da Mama binta da zasu tafi gobe. Washe gari da safe Mami ita ta aikawa da amarya da ango kayan kari. Su Asma'u kuwa suna tare da kawayen ta. Lokacin su Hafsat da Maimuna sun shirya kayan su zasu tafi. Sosai Asma'u ta hada musu kayan biki har da turmin atamfa. Har gun Mami ta raka su sukai mata sallama. Mami ta ce, a sa driver ya kai su gida. Haka ai kai kuwa. Driver sshi ya kai ko wacce har gida. Gidan ya rage daga Asma'u sai Maryam da Nusaiba da ta ce baza su tafi ba. Sai karfe daya suka shirya suka tafi gidan Amarya. Suna zuwa suka tadda Amarya a falo taci kwalliya, sai kamshi take fitar wa. Tana ganin su ta taro Asma'u sai da suka zauna kuma sai ta bata fuska. Kallon ta Asma'u tayi ta ce, "Lafiya?" "Wallahi sis baki kyauta ba wai sai yanxu ni nayi zuciya." Ta fada tana komawa gefen Maryam tana tambayar su ya gajiyar biki. Dariya Maryam tai ta kalli Nusaiba ta ce, "Yo ai ke zamuyi wa ya gajiya ko?" Nusaiba ta ce, "Lallai kam amman sai naga kamar ba ai komai ba." Dariya Asma'u tayi ta ce, "To ku ina ruwan ku." Zainab ta ce, "To waya fada muku sai kun gane anyi ko ba ai ba. Kowa da yanayin jikin sa haka nan wani yaji zafi wani bazai ji ba. Wani ya fitar da jini wani bai fitar wa. Wani tafiyar sa ta canja wani ba haka ba. Ke duk abinda zaku ji ana fadi ma wani vai san anayi ba. dan haka nidai baku jin baki na anan." Asma'u ta ce, "Dadin mutum yayi karatun bangaren lafiya kenan duk da zaku san hakan ai." Maryam ta ce, "Wai kuna so kuce duk abinda muke karantawa a littafi ba haka bane." Kai Zainab girgiza ta ce, "Ba haka bane jiki jiki ne. Wani zai ji abinda yafi na littafi wani zaiyi zazzabi wani har da suma da dai sauran su." Kai Nusaiba ta gyada na gamsuwa da abinda taji. Zainab ta ce "Ku daure ku kai budurcin ku gidan mazajen ku dan ba darajar da takai wannan a idon mijin ku. Daga ranar da ya same ki a haka zaki ji dadin rayuwa aamman da ya samu akasin haka zaki gane kuranki." Maryam ta ce, "Sis wa yakai mu. Inda muke jin labarin wacce takai budurcin ta yadda take samun jin dadi. Akasi da wanda bata kai ba wulakancin duniya ya kare akanta ba ma wacce ta zibar da mutuncin ta." Nusaiba ta ce, "Shiyasa nifa Uncle Sabir yake burgeni. Ba ruwan sa bare har ya nuna yana son wani abu agun mace ko Sis." Ta fada tana kallon Asma'u. Asma'u da jin ta sako Sabir duk jikin ta yai sanyi ta gyada mata kai ahankali. Daga haka suka cigaba da hira har Maami ta aiki da abinci da rana. Sai yamma suka tafi bayan sun gyare mata gidan. Gida suka wuce suna shiga suka zauna falo ana hira da su Momy da Mami. Sosai Mami ke jan su a jiki sai kace sun saba. Haka suka raba dare suna hira har Maryam tai bacci ta bar Asma'u da Nusaiba. Nusaiba ce ta kalli Asma'u ta ce, "Sis dan Allah in tambaye ki?" Asma'u ta kalle ta ta ce, "Ina ji!" Nusaiba ta ce "Dan Allah ki fada min gaskiya." Murmushi Asma'u tayi ta ce, "Karki damu!" Shiru Nusaiba tayi kafin ta ce, "Dan Allah mene tsakanin ku da Uncle Sabir." Murmushi Amsa'u tayi dan daman jikin ta ya bata tambayar da zatau mata kenan. Kasa tayi da kai sannan ta dago ta ce, "Malami nane, sai kuma yanzu da yake so na." Kai Nusaiba ta jinjina tai shiru. Murmushi Asma'u tayi ta ce, "Ke fa?" Ta tambaye ta ne dan bata san tana son Sabir ba. Ajiyar zuciya Nusaiba ta sauke ta ce, "Tin da na hadu dake naji kin kwanta min abu daya ne yasa na fara jin haushin ki shine ganin yadda Uncle Sabir ke miki. Gaskiya zan fada miki ni nake mutuwar son sa. Shi kam bai damu dani ba." Tayi shiru, sanna ta ci gaba da magana. Ta ce, "Sis Mu biyu iyayen mu suka haifa nice auta dan haka duk son duniya suka daura mana. Maryam kawata ce, dan Mamanah da mamanta ma kawaye ne kamar yadda Dady na da nata ma abokai ne. Mun shaku da Maryam sosai, komai nawa ta sani nima haka. Dan ko zamu hutu tare muke zuwa daga family na har nata. Tin ina primary In muka zo hutu Uncle Sabir ke burgeni ke har na girma na fara son sa. Duk yadda nake dan nuna masa ina son sa baya gane wa. Sai ni kadai nake ta haukar son sa. Ina son Uncle Sabir kamar rai na. Ina kaunar sa, wallahi amman ke kina son sa?" Nusaiba ta tambayi Asma'u. murmushi Asma'u tayi ta ce, "Sir Sabir a matsayin wa na dauke shi. Ni malami na ne," Nan ta bata labarin haduwar su da labarin ta da Yaa Aslam ta karashe labarin tana kuka. Sosai Nusaiba ta tausayawa Asma'u. Dan itama sai da tai kwalla dan itama tasan yadda so yake. Hawaye Asma'u ta goge ta ce, "Sir Sabir shike neman soyayya ta amman ni ba son sa nake ba. Amman nai miki alkawarin zan nusar da shi son da kike mas....." "A'ah......" Nusiaba ta dakatar da ita. "Karki so ma. Akan me a tinda yana son ki wallahi gara ya aure ki ina son farin cikin sa ko da zan kasance a cikin bakin ciki zan ji dadi in shi yana cikin farin ciki. Ki bari kawai Allah tabbatar da mafi alheri." Asma'u ta girgiza kai ta ce, "Bazan taba iyawa ba. Bazan iya ba kina son sa sai na san yadda ya aure ki." Nusaiba ta ce, "A'ah!" Banza Asma'u tai mata ta shige bayi tai wnaka ta dauro alwala ta zo ta saka kayan bacci ta hau kan sallaya. Tin Nusaiba na jiran ta idar suyi magana har bacci ya dauke ta. Washe gari da safe kuma suka hau shirin tafiya. Duk yadda taso su yi magana da Asma'u. Asma'u ki tayi. Da kanta ta dauke su har gida bayan Mami ta basu kayan biki suma da turamen atamfofi. Suna zuwa gida suka ci karo da Sabir shima zai fita. Kai Asma'u ta dauke tai packing sannan ta fice tayi cikin gida da sauri. Mamah ta sama a falo ta zauna a gefen ta suka gaisa. Suna cikin gaisawa su Maryam suka shigo. Zama sukai gaba daya ana ta hira sai yamma sanna Asma'u ta koma gida. A washe gari kuma Momy zata tafi. Ranar tin yamma suna tare da Momy. Momy na tambayar ta aiki sannan tana son bugar cikin ta ko akwai wanda yace yana son ta. Haka dai ta roke ta kan ta samu taje tai mata kwana biyu. Asma'u ta amsa ne kawai badan zata je ba. Har ga Allah tana son ganin Yaa Aslam sannan tana son ta san a halin da yake ciki. *HHHH INA MASU JIB GAUSHIN ASMA'U AKAN SON DA TAKEWA ASLAM. UHMM KUN SAN SO KUWA?* *MS Indabawa* [1/18, 14:33] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Part *2* Na *Maryam S Indabawa *HAJOW* *Hakuri da juriya Online writer's* Dedicated to *My lovelly Mum* *56-60* *Masoya nagode kwarai da gaske* Team *ASMA'U-ASLAM Team *ASMA'U-SABIR Hhhhh lallai kuna bani dariya yadda kuke taya Aslam ko Sabir kishi. *Inayin ku, sosai. Sis Bela'u ta hannun daman Sabir ita da Sis Sady. Inayyin ku.* *Sis Maryam Yusuf, ke da Ummu Ayda hannub faman Aslam* *Sis Fatitih ta both side an rest. *Nidai ta hannun daman Asma'u ce.* Washe gari Momy ta tafi. Haka gidan ya koma daga Mami sai Asma'u. Yaa Buhari yana zuwa da safe da dare. Ba abinda Asma'u ta sa a gaba sai aikin ta. Zumunci kuwa sun kara kullawa da Nusaiba. Yau tana zaune a garden tana sanye da wani Ash less dinkin doguwar riga. Kanta ta yafa karamin bakin mayafi. tana zaune ta zubawa wata shuka ido. Ta lula can duniyar tunani. Kamshin turaren sa da taji shi yasa ta juyo dan ganin wanene? Sir Sabir ne, yake tsaye yana sakar mata murmushi. Itama murmushin tayi. Ya zauna a kujerar dake fuskantar ta. Ido ya zuba mata, kasa tayi da kai, murmushi yayi ya ce, "Baby nah!" Shiru tayi, ya ce, "Me yasa kike boyar min ne, bayan kinsan ganin ki shi zai samin sassauci a zuciya ta." Dagowa tayi idon ta jajir ta ce, "Dan Allah Sir ka kyale ni kaima kaje wajen mai son ka." Kallon mamaki yake mata ya ce, 'Me sona kuma? Wace mai so na?" Mikewa tayi ta ce, "Kai ma kasani ai, dan Allah Sir ka so Nusaiba!" Ta fada tana tafiya. Mikewa Yayi yabi bayan ta. Kafin ya karasa ta shiga mota ta tayar harta danna horn mai gadi ya bude mata gate. Mota shima ya shiga yabi bayan ta. Gidan Zainab ta tafi. Sabir kuwa yana biye da ita a baya. Tana shiga shima ya shiga. Da sauri ta fita a mota tayi cikin gidan. Tana shiga taci karo da Zainab, kallon ta Zainab tayi ta ce, "Lafiya?" Ganin ta da tayi ta shigo a firgice, bata rufe baki ba Sabir ya shigo. Murmushi tayi ta ce, "Au ashe tare kuke?" Ciki Asma'u tayi ta barsu a nan falo. Zama yayi yana kallon hanyar da Asma'u tayi. Murmushi Zainab tayi duk da yanayin Asma'u ya bata tsoro. Lemo da ruwa ta dauki masa. Bai sha ba sai magana da ya farai mata. "Zainab ke kadai kika fi kusanci da Asma'u a kawayen ta dan Allah ki taimaka ki shawon kanta. Wallahi ina son Asma'u amman ita taki ta gane" Murmushi jin Dadi zainab tayi ta ce, "Kar ka damu zan sanar da ita." Kai ya girgiza ya ce, "Na fada mata, amman taki ta fahimci irin son da nake mata ne" "Ka barni da ita. Ina zuwa." Ta mike tayi Tana daya daga cikin dakin da ta ce na ta ne. Saboda shi karami ne kuma komai na ciki kalar ta ne. Tana kwance akan kujera idon ta lumshe hawaye na zubo mata. A ranta take cewa 'Duk Yaa Aslam ne ya jawo mata. Yanzu ita bata da wani kwanciyar hankali. Daga wancan sai wancan. To wai ita tayaya zata auri Sir Sabir bayan tasan irin son da Nusaiba ke masa. Ai kamar ta zama azaluma ne " Wata zuciyar ta ce, 'To ai shi baya son ta. In kinso shi ba wani abu bane." Juyi tayi ta bude ido ta. Zainab ta gani tsaye akan ta. Zaune ta mike ta ce, "Ya dai?" Kai ta girgiza ta zauna agefen ta. Ta ce, "Lafiya naganki haka?" "Uhnm Nida Sir Sabir ne!" Ta fada mata duk abinda ke faruwa. Zainab ma tana son Asma'u da Yaa Aslam to amman ba yadda zasu yi tinda shine ya nuna baya son ta. Tinda haka ne gwara ta amshi Sabir din tinda shi yana son ta. "Asma'u nima a gaskiya ina son ki da Yaa Aslam, but amman tinda haka ta faru ki yi hakuri ki rumgumi wanda yake son ki. Bance ki Yaa Aslam baya sonki ba, amman ki karbi Sir Sabir kuma ki yi istihara Allah zaba mafi alheri. Kiyi hakuri." Zainab ta dafa kafadar ta. Dagowa tayi da idanun ta dake zubar da hawaye ta ce, "Zainab kinsan so amman baki san zafin sa ba. Nusaiba na kaunar Sir tin tana yarinya take son sa. Tayaya xan raba wannan soyayyar da take masa. Ki tayani wannan abin ina son Sir ya fara son Nusaiba ni na hakura dashi. Ina tausayawa Sir saboda yana sona ni bana son sa, kuma ni ba kinsa nake ba, kawai dai Yaa Aslam nake so. Gwara ya auri wacce yake so zai fi jin dadin yasan yai aure da ya aure ni ni kuma zuciya ta na wani wajen ki duba magana ta Zainab nasan ke zaki fahimce ni." Ta fashe da kuka, jikin ta Xainab ta jata tana lallashin. Sai da tayi shiru sannan Ta ce, "Zan sanar da shi amman ki daina kukan nan." Kai ta gyada. Mikewa Zainab tayi ta fita. Ta sanar dashi indai yana son Asma'u to sai dai ya hada da Nusaiba. Sosai hankalin sa ya tashi. Lallabashi tayi kan yaje yai tunani sannan ya tafi gida. Wajen Asma'u Zainab ta koma. Kallon ta tayi ta ce, "Sis nai miki shishigi fa" Kallon ta Asma'u tayi ta ce, "Name fa?" "Nace indai yana son ya aure ki sai dai ya hada ke da Nusaiba." Shiru Asma'u tayi. Zainab ta ce, "Kiyi hakuri in bakiji dadi ba." "Ba haka bane. Amman ba komai." "Yauwah dan Allah sis kina rage damuwa akan Yaa Aslam. Kina addu'a Allah ya yaye miki son sa." Dagowa Asma'u tayi ta kalle ta ta ce, "Wallahi kullum sai nayi wannan addu'ar amman kamar bana yi son Yaa Aslam kara shiga ta yake. Kwanaa biyun nan ji nake kamar nai hauka dan son ganin sa da nake. Na rasa ya zanyi da son sa. Ina son Yaa Aslam kuma yana daga cikin wadan da ya koya min son sa haka." Ta fada hawaye na saukowa daga idon ta. "To ya isa. Allah yasa haka shine mafi alheri" Asma'u ta ce, "Ameen!" "Ina Mami?" Zainab ta tambaya "Uhmm Mami ta fita nima bata san nazo ba." Asma'u ta ce, "Me kika dafa ne?" "Taso muje ki gani." Ta mike ta kama hannun ta. Dining sukayi suka zauna ta fara cin abinci. Ranar har dare suna tare da yake Yaa Buhari bai dawo da wuri ba basu san har dare yayi ba. Sai karfe goma sannan ya shigo, da ta ce, zata tafi kuma ya ce, "Ba inda zata tinda Mami tasan tana gidan ta kwana kawai." Haka dole ta kwana agidan. Washe gari tare da Zainab sukai komai tai wanka ta shirya ta ce zata tafi. Hanata tafiya yayi a lokacin ya ce, Ta bari sa tafi tare gaba dayan dan zainab ma zataje gaishe da Mami. Haka ta zauna har karfe biyu sannan suka tafi gaba dayan su. A gida suka yini sai dare suka koma gida. Mami kuwa sai jan Zainab take ajiki bama da taga tana jin kunyar ta. Ita ta fiso ta zama free da ita kamar yadda Asma'u take mata. Tin daga lokacin ya zama na yar boye ke tsakanin Sir Sabir da Asma'u. A office ta maida kanta busy yadda ko ya ganta ba damar magana saboda yadda take tare da patient din ta. Haka a gida da ta shigo taga motar sa take komawa, in kuwa har ta shigo da sun gaisa take guduwa sama. In waya ya kira ma baya samu dan yanzu sai tai kwana nawa ma wayar ta a kashe. Sosai ya damu, dan yana son Asma'u yana kuma jin tausayin ta. A haka sai da suka debe wajen wata uku suna yar buyar nan. Kuma baya taba samun damar da zai ganta. Sunyi bikin Maimuna inda aka kai ta gidan mijin ta dake sabuwar gandu. Gida ne mai kyau kuma komai ya mata. Sosai Asma'u ta bata gudumawa mai yawa banda wasu abun da ta dauke mata. Asma'u da Zainab ne dai sukai mata Babbar kawa. Wanna karan ma sai da Maryam tazo, Nusaiba dai bata zo ba dan a lokacin basa kasar. Anyi biki lafiya an kai amarya gidan ta. Sosai Nazir ya amshi kaddarar Maimuna tinda daman yasan ba budurwa bace. To shi ita yake so, dan haka ya daura aniyar zama da ita da dadi ba dadi. Duk da Maimuna ba ruwan ta yanzu abinda ya ce, shi take yi. Zaman lafiya suke sosai yake faranta mata shima take faranta masa. *MS Indabawa* [1/18, 14:34] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Part *2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da juriya Online writer's* Dedicated to *My lovelly Mum* Pagr *61-65* Bangaren Sabir kuwa da abin ya ishe shi sai ya samu Yaa Buhari da batun yana son Asma'u. Duk da Yaa Buhari yafi son Asma'u su daidai ta da Aslam amman bai sa shi rashin jin dadi ba. Sosai yaji dadi dan shi yasan waye Sabir, Dan in Asma'u bata auri Yaa Aslam ba ta auri Sir Sabir ba komai. Dan ya tabbata Sir Sabir ma zai kula masa da kanwar sa. Daga nan kuwa Yaa Buhari ya tafi gida ya fadawa Mami. Mami cewa tayi, a tambayi Asma'u aji daga bakin ta. Yaa Buhari ya ce, "Aah Mami in har aka ce sai anji daga bakin Asma'u to tabbas baza ta amince ba. Kinsan irin son da takewa Yaa Aslam." Shiru Mami tayi ta ce, zata tambayi Momy taji. Momy ma sosai taji dadi dan daman ta yaba da hankalin Sabir sosai. Itama cewa tayi a bari sai abin ya matso a fada mata sanin halin Asma'u zata ce A'ah A bangaren Sabir kuwa yadda yayi zai hada Nusaiba da Asma'u dan yasan in ba haka ba Asma'u baza ta taba yadda ba. Yasan ko ba komai Nusaiba mai son sa ce dan haka zai samu duk abinda yake nema a gun ta. Amman yayi wa kansa alkawarin sai ya yayewa Asma'u halin kuncin da take ciki na rashin Yaa Aslam. Ko bata son sa shi zai zame mata farin ciki. Farin cikin da zata manta da Aslam. Nusaiba kuma ta fawalawa Allah komai. Addu'a da istihara take amman kullum son Sabir kara shigar ta yake. Duk da haka suna waya da Asma'u dan sun zama kawaye. A bangaren Zainab yanzu auren su wata bakwai yanzu tana da ciki wata hudu. Bakuga yadda Asma'u ke ji da cikin nan ba. Dan gidan ta koma da zama ma saboda taya ta aiki. Komai yi mata take. In Asma'u ta zauna hira da cikin kuwa kwa rantse da mutum take hira. Sosai Zainab ke kara lalashin ta akan zancen Sabir. Duk da yanzu ya daina mata maganar amman tana lura ba wai hakura yayi da ita ba. Yau tana gidan Yaa Buhari ake sa ranar bikin ta da Sabir, an sanya rana shekara daya, saboda so ake a hada bikin da na Nusaiba akai masa mata biyu a rana daya. Ya sanar da su manufar sa tayin hakan kuma sun yadda dan sun san kafiyar Asma'u. In ta ce, "Eh!" Ba wanda zai sa ta ce, "A'ah!" In kuwa aka matsa to za'a ga ba dai dai ba. Duk da Momi bata so hakan ba. Amman ta yadda dan san halin yar tata. Momy ma tazo komai anyi shi cikin kwanciyyar hankali. Asma'u kuwa tana can bata san ana yi ba. Duk da Zainab ta sani. Sai dai Asma'u kanji yawan faduwar gaba. Momy ce zaune a falo tare sa Mami da Yaa Buhari. Bayan sun gama tsara komai ne, Momy ta kalli Buhari ta ce, "Buhari kun yi maganar Yayan ka da Mami kuwa." Dagowa yayi ya dan jima kafin ta ce, "Wallahi Momy bamuyi ba. Kuma abin na raina kullum. Bama Asma'u da nake son sanar wa." Kai Momy ta girgiza ta ce, "Kasan sai a shekaran jiya na fada yadda da ba haka matar Aslam ta bar shi ba. Kaga yadda take masa kuwa ta maida shi bawa fa, ba abinda yyake iya yi sai da izinin sa. Aslam duk ya rame." Tayi shiru ta ce, "Jiya da na aika a kira min shi cewa tayi bazai zo ba, sai da ta shiga ciki yake bawa dan aiken hakuri kan ya bani hakuri tinda ta ce, bazai zo ba. Ni da ganin Aslam fa sai nai wata. Kudi kuwa account dinsa na hannun ta. Dan Allah Buhari yazamuyi Na fison muyi abu wanda baza mu.kaucewa Allah ba. Dan ni bana son bin malaman nan su fara juyawa mutun tunani da canfe canfen su." Kai Mami ta gyada ta ce, "Innaillilahi wa inna illahir rajiun. Yanzu yadda ta maida Aslam din kenan. To Allah kai mana magani." "Ameen!" Momy da Buhari suka amsa da. Buhari na komawa gida ya samu Asma'u ya ce, "Asma'u ina son magana da ke!" Ganin da yadda yai mata maganar yasa ta san magana ce mai mahimmanci. Kallon sa tayi ta ce, "To ina ji." Tana komawa gefen sa. Kallon ta yayi, ya ce, "Ina son ki sa a ranki duk abinda ya faru da bawa mukaddari ne Allah ya riga da ya tsara, sannan ina fatan duk abinda yya same ki zaki amsa hannu bibiyu" Kai ta gyada ta ce, "Insha Allahu." Ya ce, "Magana zan miki guda biyu kuma kowa ce ina son ki amshi abinda zan fada miki." Sai da ta dago ta kalle shi sannan ta ce, "Insha Allahu zzan dauka." Gyaran murya yayi sanann ya ce, "Sabir!" Jin suna da ya ambata yasa kirjin ta dukan uku. Ta dago da sauri. Kai ya dauke ya ce, "Sabir ya same ni da zance yana son ki. Dan haka mun ba shi dama dan nasan in take ce baza ki amshe sshi ba. Yau aka sa ranar bikin ku nn da wata shekara za ayi bikin ku insha Allahu." Kasa tayi da kai tana zubar da hawaye. To ita dan ta dan ta auri Sir Sabir mene, tinda ta rasa wanda take so ma. To amman fa ita Nusaiba take ji. Kuma bazata iya bujurewa maganar su Mami ba. Tana son Yaa Aslam amman kenan ya zama dole ta hakura dashi. Tinda tasan ba yadda zai tana da aure ta so wani ba kuma. Duk maganar da Yaa Buhari yacigaba da fadi ba ji take ba. Sai da taji ya ambaci Yaa Aslam sannan hankalin ta ya dawo kansa. "Tinda naje Abuja naga halin da yake ciki ba san ba haka matar sa ta bar shi ba. Sai kuma yau da Momy tazo take fadan halin da yake ciki. Asma'u mune kadai yan uwan Yaa aslam dole mu tsaya akan sa da addu'a sannan da wani abun da muka sani na tsarin jiki." Tinda ya fara magana take kuka har yanzu da ya kare abinda yake fadi "Kar ki diba abinda yai miki ki 'ki taya shi da addu'a kinsan Yaa Aslma ya so ki a baya to yanzu ma ki dauka kaddara kuce tasa kuka rabu " Shiru tayi amman sai hawaye dake ambaliya a idon ta. "Asma'u!" Ya kira sunan ta. Dagowa tayi da idanun ta da suka rine da hawaye sukai jajir da su. "Mene na kuka? Sabir din ne bakya so?" Kai ta girgiza "To Yaa Aslam din baza ki taya da addu'a ba?" Shima kai ta girgiza. "To yi hakuri ki daina kuka kinji." Kai ta gyada masa. Mikewa tayi jiki a sanyaye ta shiga dakin da take kwana. Kayan ta ta fara hadawa tana cikin hadawa Zainab ta shigo. Kallon ta ta tsaya ganin tana debo kaya daga cikin durowa zuwa cikin akwatin ta. "Lafiya?" Zainab ta tambaya. "Tafiya zanyi. Sis yanzu a gida an daina so na mai sona a duniya mutum daya ne, kuma ya mutu wanda na dauka shima yana sona din ya daina, to Mami ma da Yaa Buhari sun daina. Wai har sun gaji dani zasu aurar dani ba tare da ina son sa ko an tambayen ra'ayi na ba. Zan bar muku gidan ku ina jin na tare muku wani abu shine yake son nai aure na bar muku gida. Zan tafi gida nasan can Mami baza ta koren ba dan nasan shi zai kai mata maganar Sir Sabir." Buhari da yana tsaye bakin kofa shima ya shigo. Ya ce, "Ko daya kanwata. Bazan taba daina son ki ko gajiya da ke ba. Ki fuskance ni. Nasan dai ke ba yarinya bace karama kinsan komai. Bai kamata ace kin kai yanzu ba aure ba. kin gama karatu har kina aiki ai gwara kiyi aure tinda kin samu mai son ki. Kada ki manta da fa tini kina gidan ki wa yasani ma ko da ciki ko 'da. Mutunci 'ya mace gidan mijin ta fa." Fuska ta rufe saboda kunya. Yaa Buhari ya ce, "Kiyi hakuri ki karbi zabin mu insha Allahu zaki ji dadi." Kai ta gyada. Ya ce, "To ki mai da kayan." Kai ta make masa, ta ce, "Ni dai gida." Murmushi yayi ya ce, "Husnah daru." Kai ta gyada ta ce, "Naji." Ya ce, "Kya bari dai gobe ko?" Kai ta girgiza masa. Duk yadda yaso ta zauna ki tayi. Da zai matsa mata ma sai ta saka masa kuka. Dole suka bar ta ta tafi ba dan sun so ba. Tana zuwa gida ta shige dakin ta ta rufe. Kwanciyya tayi ta rasa wane tunanin zatai tunanin aure da za ai mata ne ko tunanin halin da Yaa Aslam yake ciki ne. Mikewa tayi ta fada bandaki alwala tayo ta fito ta dinga yin nafila. Ta jima tana yi sannan ta dauko kur'ani ta karanta, addu'a tayi masa sosai. Sannan ta zame agun bacci ya dauke ta. Buhari ne ya fadawa Mami, Asma'u ta taho wannan yasa ta zo daki ta dduba. A kwance ta same ta a kasa, idanun ta sun kumbura Tabata Mami tayi ta bude idanun ta. Jajir suke sai kace gauta. Mami ta ce, "Tashi ki hau kan gado." Mikewa tayi ta hau kan gado. Fita Mami tayi ta kawo mata fura da ta dama. Kawo mata tayi ta amsa ta sha. Mami na fita ta koma ta kwanta. Bacci ne yaki zuwa wanna yasa ta mike tana ta addu'a. *MS Indabawa* *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Part *2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da juriya Online writer's* Dedicated to *My lovelly Mum* Pagr *61-65* Bangaren Sabir kuwa da abin ya ishe shi sai ya samu Yaa Buhari da batun yana son Asma'u. Duk da Yaa Buhari yafi son Asma'u su daidai ta da Aslam amman bai sa shi rashin jin dadi ba. Sosai yaji dadi dan shi yasan waye Sabir, Dan in Asma'u bata auri Yaa Aslam ba ta auri Sir Sabir ba komai. Dan ya tabbata Sir Sabir ma zai kula masa da kanwar sa. Daga nan kuwa Yaa Buhari ya tafi gida ya fadawa Mami. Mami cewa tayi, a tambayi Asma'u aji daga bakin ta. Yaa Buhari ya ce, "Aah Mami in har aka ce sai anji daga bakin Asma'u to tabbas baza ta amince ba. Kinsan irin son da takewa Yaa Aslam." Shiru Mami tayi ta ce, zata tambayi Momy taji. Momy ma sosai taji dadi dan daman ta yaba da hankalin Sabir sosai. Itama cewa tayi a bari sai abin ya matso a fada mata sanin halin Asma'u zata ce A'ah A bangaren Sabir kuwa yadda yayi zai hada Nusaiba da Asma'u dan yasan in ba haka ba Asma'u baza ta taba yadda ba. Yasan ko ba komai Nusaiba mai son sa ce dan haka zai samu duk abinda yake nema a gun ta. Amman yayi wa kansa alkawarin sai ya yayewa Asma'u halin kuncin da take ciki na rashin Yaa Aslam. Ko bata son sa shi zai zame mata farin ciki. Farin cikin da zata manta da Aslam. Nusaiba kuma ta fawalawa Allah komai. Addu'a da istihara take amman kullum son Sabir kara shigar ta yake. Duk da haka suna waya da Asma'u dan sun zama kawaye. A bangaren Zainab yanzu auren su wata bakwai yanzu tana da ciki wata hudu. Bakuga yadda Asma'u ke ji da cikin nan ba. Dan gidan ta koma da zama ma saboda taya ta aiki. Komai yi mata take. In Asma'u ta zauna hira da cikin kuwa kwa rantse da mutum take hira. Sosai Zainab ke kara lalashin ta akan zancen Sabir. Duk da yanzu ya daina mata maganar amman tana lura ba wai hakura yayi da ita ba. Yau tana gidan Yaa Buhari ake sa ranar bikin ta da Sabir, an sanya rana shekara daya, saboda so ake a hada bikin da na Nusaiba akai masa mata biyu a rana daya. Ya sanar da su manufar sa tayin hakan kuma sun yadda dan sun san kafiyar Asma'u. In ta ce, "Eh!" Ba wanda zai sa ta ce, "A'ah!" In kuwa aka matsa to za'a ga ba dai dai ba. Duk da Momi bata so hakan ba. Amman ta yadda dan san halin yar tata. Momy ma tazo komai anyi shi cikin kwanciyyar hankali. Asma'u kuwa tana can bata san ana yi ba. Duk da Zainab ta sani. Sai dai Asma'u kanji yawan faduwar gaba. Momy ce zaune a falo tare sa Mami da Yaa Buhari. Bayan sun gama tsara komai ne, Momy ta kalli Buhari ta ce, "Buhari kun yi maganar Yayan ka da Mami kuwa." Dagowa yayi ya dan jima kafin ta ce, "Wallahi Momy bamuyi ba. Kuma abin na raina kullum. Bama Asma'u da nake son sanar wa." Kai Momy ta girgiza ta ce, "Kasan sai a shekaran jiya na fada yadda da ba haka matar Aslam ta bar shi ba. Kaga yadda take masa kuwa ta maida shi bawa fa, ba abinda yyake iya yi sai da izinin sa. Aslam duk ya rame." Tayi shiru ta ce, "Jiya da na aika a kira min shi cewa tayi bazai zo ba, sai da ta shiga ciki yake bawa dan aiken hakuri kan ya bani hakuri tinda ta ce, bazai zo ba. Ni da ganin Aslam fa sai nai wata. Kudi kuwa account dinsa na hannun ta. Dan Allah Buhari yazamuyi Na fison muyi abu wanda baza mu.kaucewa Allah ba. Dan ni bana son bin malaman nan su fara juyawa mutun tunani da canfe canfen su." Kai Mami ta gyada ta ce, "Innaillilahi wa inna illahir rajiun. Yanzu yadda ta maida Aslam din kenan. To Allah kai mana magani." "Ameen!" Momy da Buhari suka amsa da. Buhari na komawa gida ya samu Asma'u ya ce, "Asma'u ina son magana da ke!" Ganin da yadda yai mata maganar yasa ta san magana ce mai mahimmanci. Kallon sa tayi ta ce, "To ina ji." Tana komawa gefen sa. Kallon ta yayi, ya ce, "Ina son ki sa a ranki duk abinda ya faru da bawa mukaddari ne Allah ya riga da ya tsara, sannan ina fatan duk abinda yya same ki zaki amsa hannu bibiyu" Kai ta gyada ta ce, "Insha Allahu." Ya ce, "Magana zan miki guda biyu kuma kowa ce ina son ki amshi abinda zan fada miki." Sai da ta dago ta kalle shi sannan ta ce, "Insha Allahu zzan dauka." Gyaran murya yayi sanann ya ce, "Sabir!" Jin suna da ya ambata yasa kirjin ta dukan uku. Ta dago da sauri. Kai ya dauke ya ce, "Sabir ya same ni da zance yana son ki. Dan haka mun ba shi dama dan nasan in take ce baza ki amshe sshi ba. Yau aka sa ranar bikin ku nn da wata shekara za ayi bikin ku insha Allahu." Kasa tayi da kai tana zubar da hawaye. To ita dan ta dan ta auri Sir Sabir mene, tinda ta rasa wanda take so ma. To amman fa ita Nusaiba take ji. Kuma bazata iya bujurewa maganar su Mami ba. Tana son Yaa Aslam amman kenan ya zama dole ta hakura dashi. Tinda tasan ba yadda zai tana da aure ta so wani ba kuma. Duk maganar da Yaa Buhari yacigaba da fadi ba ji take ba. Sai da taji ya ambaci Yaa Aslam sannan hankalin ta ya dawo kansa. "Tinda naje Abuja naga halin da yake ciki ba san ba haka matar sa ta bar shi ba. Sai kuma yau da Momy tazo take fadan halin da yake ciki. Asma'u mune kadai yan uwan Yaa aslam dole mu tsaya akan sa da addu'a sannan da wani abun da muka sani na tsarin jiki." Tinda ya fara magana take kuka har yanzu da ya kare abinda yake fadi "Kar ki diba abinda yai miki ki 'ki taya shi da addu'a kinsan Yaa Aslma ya so ki a baya to yanzu ma ki dauka kaddara kuce tasa kuka rabu " Shiru tayi amman sai hawaye dake ambaliya a idon ta. "Asma'u!" Ya kira sunan ta. Dagowa tayi da idanun ta da suka rine da hawaye sukai jajir da su. "Mene na kuka? Sabir din ne bakya so?" Kai ta girgiza "To Yaa Aslam din baza ki taya da addu'a ba?" Shima kai ta girgiza. "To yi hakuri ki daina kuka kinji." Kai ta gyada masa. Mikewa tayi jiki a sanyaye ta shiga dakin da take kwana. Kayan ta ta fara hadawa tana cikin hadawa Zainab ta shigo. Kallon ta ta tsaya ganin tana debo kaya daga cikin durowa zuwa cikin akwatin ta. "Lafiya?" Zainab ta tambaya. "Tafiya zanyi. Sis yanzu a gida an daina so na mai sona a duniya mutum daya ne, kuma ya mutu wanda na dauka shima yana sona din ya daina, to Mami ma da Yaa Buhari sun daina. Wai har sun gaji dani zasu aurar dani ba tare da ina son sa ko an tambayen ra'ayi na ba. Zan bar muku gidan ku ina jin na tare muku wani abu shine yake son nai aure na bar muku gida. Zan tafi gida nasan can Mami baza ta koren ba dan nasan shi zai kai mata maganar Sir Sabir." Buhari da yana tsaye bakin kofa shima ya shigo. Ya ce, "Ko daya kanwata. Bazan taba daina son ki ko gajiya da ke ba. Ki fuskance ni. Nasan dai ke ba yarinya bace karama kinsan komai. Bai kamata ace kin kai yanzu ba aure ba. kin gama karatu har kina aiki ai gwara kiyi aure tinda kin samu mai son ki. Kada ki manta da fa tini kina gidan ki wa yasani ma ko da ciki ko 'da. Mutunci 'ya mace gidan mijin ta fa." Fuska ta rufe saboda kunya. Yaa Buhari ya ce, "Kiyi hakuri ki karbi zabin mu insha Allahu zaki ji dadi." Kai ta gyada. Ya ce, "To ki mai da kayan." Kai ta make masa, ta ce, "Ni dai gida." Murmushi yayi ya ce, "Husnah daru." Kai ta gyada ta ce, "Naji." Ya ce, "Kya bari dai gobe ko?" Kai ta girgiza masa. Duk yadda yaso ta zauna ki tayi. Da zai matsa mata ma sai ta saka masa kuka. Dole suka bar ta ta tafi ba dan sun so ba. Tana zuwa gida ta shige dakin ta ta rufe. Kwanciyya tayi ta rasa wane tunanin zatai tunanin aure da za ai mata ne ko tunanin halin da Yaa Aslam yake ciki ne. Mikewa tayi ta fada bandaki alwala tayo ta fito ta dinga yin nafila. Ta jima tana yi sannan ta dauko kur'ani ta karanta, addu'a tayi masa sosai. Sannan ta zame agun bacci ya dauke ta. Buhari ne ya fadawa Mami, Asma'u ta taho wannan yasa ta zo daki ta dduba. A kwance ta same ta a kasa, idanun ta sun kumbura Tabata Mami tayi ta bude idanun ta. Jajir suke sai kace gauta. Mami ta ce, "Tashi ki hau kan gado." Mikewa tayi ta hau kan gado. Fita Mami tayi ta kawo mata fura da ta dama. Kawo mata tayi ta amsa ta sha. Mami na fita ta koma ta kwanta. Bacci ne yaki zuwa wanna yasa ta mike tana ta addu'a. *MS Indabawa* [1/18, 14:35] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Part *2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* ?? *HAJOW* ?? *Hakuri da juriya Online writer's* Dedicated to *My lovelly Mum* Page *66-70* *HAPPY BIRTHDAY PRINCESS AMRAH. WISH MORE YEARS AHEAD+ MIJI NA GARI+ YA'YA MASU ALBARKA+ RAYUWA MAI AMFANI+ RESULT MAI KYAU.* *AMEEN* Tin daga lokacin rayuwar Asma'u ta kara komawa shiru shiru, dan daga wajen aiki sai ibada da ta sa a gaba. Addu'a kuwa kullum yi take Allah ya yayewa Yaa Aslam abinda yake damun sa. Haka nan addu'a ta daya ce Allah ya zaba mata mafi alheri. Duk ta rame, Mami ma ta rasa kanta. Dan ko zaman falo ta daina kullum tana daki kan sallaya. Wayar ta kuwa ta kashe ta gaba daya. Duk yadda Sir Sabir yake son ganin ta ko kiran ta awaya ba dama Dan sai ya yini a asibiti bai ganta ba. In ma a gidan ne haka baya taba ganin ta. Yau kamar kullum zaman dakin ya ishe ta gashi bata sallah. Carbi ne a hannun ta, ta mike ta fita tayi garden. Tana shan kwana Sir Sabir na shigowa. Hango ta da yayi yasa yabi vayan ta. Tana zama shima ya karasa wajen ya zauna. Kallon ssa tayi ta dan yi murmushi. Ta ce! "Ina yini?" Ajiyar zuciya ya sauke ya ce, "Wallahi kina wahalar dani." Shiru tayi ta kasa ce masa komai. Ya ce, "Husnah kiyi hakuri wallahi tausayin ki nake ji shiyasa nayi duk abinda na aikata amman kiyi hakuri. Bayan nan kuma Nusaiba da kike magana akai na miki alkawarin tare za'a hada bikin ku." Dagowa tayi da sauri ya gyada mata kai, ya ce, "Eh! Tare aka saka ranar ku." Kai tai kasa da shi. Tin daga lokacin bata kara magana ba. Tana can tunani wai su biyu za'ai bikin su. A ranta ta ce, 'To mene ni da ba son mijin nake ba.' Duk maganar da yake mata ma ba ji take ba tana can duniyar tunani. Haka har ta jiyo kiran sallah magariba. Wannan yasa ta mike tana ce masa, "Sai anjima." Kallon ta yayi ta shige cikin gida. Kai ya girgiza ya rasa ya zai yi ya shawo kan Asma'u. Tana zuwa ciki ta kunna wayar da wajen sati biyu rabon da ta kunna. Text din Nusaiba da Zainab da Maryam duk ta gani. Na Nusaiba ta bude taga sakon akan sa ranar da akai musu ne. Tsaki tayi najin wai Nusaiba na murna dan zasu auri Sabir tare. Wayar ta kashe ta jefa ta gefe daya ta saka kuka. Sai da tayi mai isar ta sanna ta mike ta shiga bayi ta wanke fuskar ta. Haka rayuwar ta ta kasance, har Zainab ta haihu ta haifi dan ta na miji. Sunan Dady aka saka masa, Asma'u na kiran sa da Dady. Su kuma suna kiran sa da Aiman. Sosai Amsa'u ke son Aiman. Dan kullun sai taje ta ganshi. Duk da, da ta ganshi take tafiya. Ko zainab yanzu ta kasa gane kan Asma'u. Dan sai taje gidan daga gaisuwa shikenan. A haka har lokacin bikin su ya rage wata biyu da Sabir. Amman zan iya cewa ko sun hadu daga gaisuwa shikenan dan ko zai yi magana ba jin sa ma take ba. Haka nan su Mami da Momy da Zainab suke ta shirye shiryen bikin. Banda ita da ko an tambaye ta abu bata bada asma. Takanas Nusaiba tazo dan jin me dame zasu yi amman sam Asma'u hata bata amsa ba. Sai gun Zainab taje suka tsara komai da ita. Ranan tana zaune tana lalluben littafan isilamiyyar ta sai da lalubo wani littafi. Littafin da ta dade tana neman dan anan ta rubuta wasu abubuwa ta. Tana Budewa taga littafan addu'oin da Malamin su ke basu ne tana rubutawa a ciki. Dubawa ta farayi sai ta gano wani rubutu da ta rubata 'Karya sihiri' Dubawa tayi ta ga abinda ta rubuta. 'Ya hallata a karya sihiri amman ba ayi ta ko wacce hanya sai abinda ya shafi hadisi ba aje gun wani dan yin wani abu ba. Da farko wanda akai wa ya jimanci karatum Alkur'ani, Amanarrasuli, Ayatul kursiyyu, Falaki, Nas, Ahad, Bakara, sannan mutum zai samu habbatus sauda, da zam zam sai a karanta, fatiha, aciki ya shafe jikin sa. Ya na karanta suratul mulki, jinnu, yusuf, sannan ya samu zam zam, zuma a karanta Wasafati a ciki ana sha. Da yadda Allah komai akai wa mutum zai warke." Tana gani ta mike da sauri dauki wayar ta. Kunnawa tayi ta lalubi number Momy ta tura mata da yadda zata yi sannan ta koma ta zauna. Tana zama sa ga kiran Sabir nan tsaki tayi ta ce, "Daga kunna waya." Dauka tayi ta kara a kunnen ta, tai sallama cikin sanyin murya. Amsawa yayi daga dayan bangare. Ya ce, "Kina lafiya?" Kai ta gyada, sai kuma ta tuna baya ganin ta, ta ce, "Lafiya!" Ya ce, "Asma'u yanzu haka kike ganin rayuwa zata tafiyu, aure fa zamu yi amman kwata kwata kin kasa sakin jikin ki dani sauran fa wata daya. Dan Allah ki tausaya min." Tausayin sa ne ya kamata, ya ce, "Wallahi Husnah nai miki alkawarin samar miki dukkan farin cikin ki ko da zai zame min bakin ciki. Ki yadda dani." Shiru tayi dan ta saba da irin wadan nan kalaman wajen Yaa Aslam. Amman yanzu ina kalaman sukai. Taso ace Yaa Aslam ne ke kara fada mata wadan nan kalaman. Sai dai kash ba shi bane, to tana fatan Allah yasa hakan. Alkawarin rikan da ya dinga daukar mata sai take ganin kamar Yaa Aslam ne. Wannan shi ya dan sasauta mata ta sauko saboda tausayin sa da take ji. A haka ya roke ta, akan ta daina kashe wayar ta. Sannan kuma yana son ta fada masa abubuwan da take bukata. Ba laifi ta dan saki jiki sunyi waya amman fa duk sai dai in shi ya tambaye ta abu. Suna gamawa ya kira Nusaiba ita ma suka dan gaisa. A bangaren Aslam kuwa abin ba dadin ji, dan pretty ta zame masa karfen kafa. Baya iya komai sai da cewar ta. Duk da sai tai wata nawa bata gari amman ko kala baya iya cce mata. Sai dai in shi zai fita ta hana shi fita. Yanzu ma tayi tafiyar da ta saba ne, shine ya samu damar zuwa gaida Momyn sa. Yana zuwa Momy ta bashi hadin abinda Asma'u ta turo mata ya sha. Sannan ta bashi sauran ta ce, yana amfani dasu Sosai ta masa nasiha kan ya dage da addu'a da karatun Alkur'ani. Shi sai a lokacin ma ya tuna da duk ya manta bayayi. Mutumin da a da sai ya kwana a kan sallaya. Kwana biyun da tayi bata nan sosai ya samu ya dawo hayyacin sa. Dan Mami da ruwan da ta bashi ya kare take kara aika masa da wani. Ba laifi kuma yana tashi yai sallah da addu'oin neman tsari. Sai gashi ya fara dawo dai dai, duk yadda ya firgice yanzu ya dawo dai dai. Dan kullum zai je gaishe da Momy, kuma Yanzu yana yawan tunanin ina Asma'un sa. Sai da Pretty tai sati biyu sannan ta dawo. Tana shigowa gida ta tadda baya nan. Nan ta tanadi masifar da zatai masa. Sai wajen karfe goma ya baro gidan Momyn sa. Yana shigo yai cikin gida. A falo ya same ta kafa daya kan daya. Kallon ta yayi ya watsar yayi hanyar bangaren sa "Mallam baka ganni bane?" Ta tambaye sa Banza yai mata dan shi bai zata da shi take bama. Mikewa tayi ganin ya shige ba tare da ya dawo ba. Bayan sa ta bi, ban san me ya faru ba sai ihun ta na jiyo ta fito daga dakin sa da gudu. Zama tayi tana defe kunci saboda zafin marin da taji. Kallon dakin tayi tana tunanin ayyan kuwa Aslam ne wannan. Aslam har ya daga hannu ya mare ta. Sosai take jin jina Abin. Shi kuwa wanka yayi yai alwala ya saka kayan baccin sa zama yayi yana mamakin har tayaya ya bari yarinyar nan ta raina shi haka. Ya jima yana tunani sannan ya mike ya tada sallah. Ya jima yana sallah sannan ya zauna yyana addu'a, maganin shi ya sha ya dauki al kur'ani yana karanta Suratul Bakara. Tin da ya fara karantawa yaji kansa na juyawa amman bai dai na ba. Haka ya cigaba da yi. Har ya daina jin abinda yake ji. Sannan kuma ya kwannta. Abin mamaki da ya rufe idon sa sai yaga Asma'u, Mikewa yayi ya dauko wayar sa number ta yai dailing amman a kashe hakura yayi ya koma ya kwanta. *Hhhh toh fah ya kk ji chapte?* *MS Indabawa* [1/18, 14:35] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Part *2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da juriya Online writer's* Dedicated to *My lovelly Mum* *71-75* *Na gaishe ku yan kungiyar *HAJOW* ubangiji Allah ya kara basira da daukaka. Ina minyin ku irin da yawan. Soyayyar ku bazata misaltu ba. Sai dai Addu'a Allah ya bar mu tare har abada har a gidan Aljanna. Allah ya hada mu kamar yadda muke anan ma. Ameen.* *Momyn mu, Nafisa Sulaiman (Hajiya Nafeesa) a koda yaushe ina yaba karamci da soyayyar gare mu. Allah ya raya zuri'a Allah dada lafiya da nisan kwana. Ameen* Haka canji ya dinga samuwa wajen Aslam. Dan har fita yake hana Munasha. Sosai ta shiga hankalin ta. Dan taga ya dawo Aslam din shi na farko. Wanda kwarjinin sa ya dadu, shi wani lokacin Mamakin mai ya hada shi da Pretty yake yi Haka zai je gun Mami yai ta cewa, "Mami number Asma'u nake nema." Sai dai Mami ta dauke kai in ya ishe ta. Ta ce, "Me zakai mata?" "Mami ina son jin muryar ta ne, ina son sanin halin da take ciki." Dariya Mami take in ya fadi haka. Tace, "Aslam sai yanzu kake son sanin halin da take ciki, a kalla shekara biyu rabon ku baka taba tunanin haka ba sai yanzu." Yana mamaki in Mami ta ce, sun shekara biyu basa tare dan shi gani yake kwana ki ne. Ganin yadda Aslam ya daina sakar mata dan ba inda take zuwa ma. Kuma duk masu aikin nan ya rage su. Gashi ya amshi kudin sa dake gun ta. Wannan ya tada mata da hankali har ta dau aniyar koma wajen Bokan ta. Shirye shirye tafiya ta fara ba tare da tasanar da shi ba. Haka ta dauki hanyar nijar. Agidan kawar ta ta sauka daga nan ta nufi gun bokan ta. Yana ganin ta ya fara dariya dan yasan aiki ya lalace yanzu kuma damar sa ce. Da ta fada masa damuwar ta yayi dariya ya ce, "In zaki yadda ki bar Aslam shine yafi miki alheri. Kizo gareni muyi rayuwa mai dadi." Zabura tayi jin abinda bokan yake fadi. Mikewa tayi tana nuna shi da yatsa. Ta ce, "Allah ya kiyaye min na aure ka. na aure ka nace na auri wa? Baka da hankali." Ta tofar da yawo tayi gaba. Dariya yayi ya ce, "Dani kike zaki dawo da kafafun ki.' Haka ta tafi aka rakata wanin wajen, Malamin bai mata aiki ba sai da ya kusance ta. Haka taa dawo gida da sa ran ganin canji ammn abinda Aslam yai mata ya kara tada mata da hankali. Dan takardar saki ya mika mata. Har saki uku. Sosai ta firgita. zatai masa magana ya zare mata ido yace ta tafi zai aiko mata da kayan ta. Gida ta tafi tana kuka kai kace babar ta ce ta rasu. Aslam kuwa ji yayi kamar an dauke masa duk wani nauyi akan sa. Yanzu damuwar sa daya ita ce Asma'u. Asibitin sa, da baya zuwa shi ya koma ya tada shi. Sai da ya dai dai ta komai sannan ya fara shirin tafiya Kano. Pretty kuwa Momah ta ce ta dinga kwantar mata da hankali kan zasu san abinda zasuyi ta koma gidan ta. Sosai ta ji dadi. Haka ta koma karuwancin ta duk da ita ta fison tayi aure ta huta. Duk wanda yazo mata ta ce ya fito baya kara dawowa. Haka nan ko a cikin yan harkar su haka abin yake. Ita auren kisan wuta take son tayi. Tunawa da bokan ta da tayi ta ce, "Bazata gun sa ba tasan ba zai sake ta ba ko ya aure ta." Shikuwa bata san yana can yana shirye shiryen yadda zai shawo kanta ba. Rannan tana kwance akan gado ta mike zunbur. Mayafi ta saka ta fito sai tasha. Motar nigar ta shiga suna sauka tayi wajen Bokan ta. Da kuka ta ke ce masa ya taimaka ya aure ta. A haka dai ta zauna a gun sa suna rayuwa banza dan ba aure sukai ba. Asma'u kuwa abu na kara rikice mata duk da tana son sa son Sabir a ranta amman kuma ita tana son Aslam fa. Ga shi lokacin biki sai karatowa yake yanzu sauran sati biyu. Yau tin da ta tashi take jin faduwar gaba amman ta rasa ko ta macece. A haka tai wanka ta shirya ta tafi aiki. A wajen aikin ma ba wani aiki tayi ba sai kwanciyya. Tana tashi kuwa taiwa Mami waya ta tafi ganin Dady. Gidan Yaa Buhari ta tafi can ta zauna tana tai wa Aiman wasa. Yaro ya fara girma kyakyawa dashi. Dan farin Baban sa ya dauko. Yau tin safe Aslam yayo wa kano linkaya. Da wajen karfe biyu ma yana cikin kano. Gidan su Asma'u ya wuce kai tsaye. Yana zuwa Mami ta tarbe shi kamar yadda suka saba. Zama sukai suna hira, yana tambayar Buhari. Mami take fada masa haihuwa yaron da akayi ma. Sosai ya taya shi murna dan Aslam akwai son yara. Shiru yayi kafin ya dago ya ce, "Mami! Husnah fa." Murmuahi Mami tayi ta ce, ta tafi aiki daga can kuma tace zata gidan Buhari." Kai ya gyada ya ce, "Mami daman akan Husnah nazo." Gyara zama Mami tayi ta ce, "To ina ji." Kasa yayi da kai ya ce, "Mami wallahi ban san ya akai har na auri Pretty ba bayan duk duniya ba wacce na tsana sama da ita, wallahi Mami bansan me ya raba ni da Asma'u ba, sai kawai tsintar kai na nayi da rasa ta. Mami ki taimake ni ki bawa Husnah hakuri ta zo muyi aure." Tinda ya fara magana Sabir da ya ke tsaye bakin kofa yake jin sa. Juyawa yayi ya shiga motar sa yayi gidan Buhari. Mami ganin hankalin sa ya tashi yasa ta ce, "Kaga Aslam ka kwantar da hankalin ka, kasan komai mukadari ne, ni kai na zan so Asma'u ta aure ka. Amman in haka Allah ya tsara zan fi kowa murna, haka nan in akasin haka ne ma bazan yi bakin ciki ba tinda nasan kana tare da ita a matsayin dan uwa. Yanzu dai ka kwanar da hankalin ka kaji." Kai ya gyada. Mami ta kawo masa abinci ya ci sannan ya hau sama Dakin Asma'u ya fara shiga, kamshin ta da ya missing shi ya fara sheka yana lumshe idanu. Kan gadon ta ya fada yana shinshinar sa Ya jima a Kwance sanna ya mike yana kurawa wani hoton ta kallo. Ba karamin kyau tayi ba, ita da wani jariri. Ga dukkan alama yasan 'dan Buhari ne. Murmushi yayi ya ce, "Su Husnah da 'da." Mikewa yayi ya fita ya sauka kasa. Mami ya sama ya ce, "Mami A wanne gida Buhari yake?" Mami ta ce, "Can Rijiyar zaki ne!" Kai ya gyada ya fita da yake yasan duk gidan jen su. Can ya nufa kai tsaye da zumudin ganin Asma'u. Asma'u da tinda tazo tana dakin ta da Dady dan har bacci sukai suka tashi sukai wanka. Kwalliya tayi sosai wacce ta dade bata yi ba. Haka ma tai wa Aiman kwalliya dan fita take son suyi. Tana fita falo ta samu Sabir a zaune. Dan murmushi tayi ta zauna daga nesa dashi. Ta ce, "Yaushe kazo?" Ya ce, "Maman Baby kenan tun dazu. Ina zaku kukai wannan kwalliya haka." Murmushi tayi ta ce, "Unguwa zamu ni da Dady nah." Kallon ta yayi a ransa ya ce, "Kar dai ace Aslam taiwa kwalliyar nan." Mikewa tayi ta shiga dakin Zainab bata nan. Kitchen ta shiga, ta ce, "Mumyn Dady mu xamu tafi unguwa." Juyawa Zainab tayi ta ce, "Au daman zuwan da Sir yayi kenan." Hararar ta tayi ta ce, "Ba tare zamu fita ba." Baki Zainab ta kama ta ce, "Oh wai ke ki ta fita da yaro sai kace matar aure ai sai ya kashe miki kasuwa. Oh ko da yake an siyar daman." Dariya Asma'u tayi ta ce, "Kinyi kidan ki kinyi rawar ki." "To a dawo lafiya. Kema nan da yan wattan ni dai zaki rike kanin Dady." Zainab ta fada tana dariya "Allah ya isa sis ke kin fiya abu wallahi." Ta fita tana cewa. "Ba za mu kawo miki tsara ba ba." Inda ta bar shi anan ta same shi. "Sir sai mun dawo!" Ta fada tana yin gaba. Mikewa yayi ya ce, "Nima gida zan tafi." Ta shiga mota ta saka Dady a abin zaman sa. Sanan ta koma driving sit din ta. Ta zauna. Taga ya leko, ya ce, "Gobe zasu kawo lefe fa amarya ta." Murmushi ta dan yi ta ce, "To Allah ya kaimu." "Ameen! Yau an kai na Nusaiba." Ta ce, "Masha Allah Allah ya sanya alheri ya bada zaman lafiya." "Ameen a dawo lafiya." Ya mike yana daga mata hannu. Hannu itama ta daga masa ta tada motar ta fice. Motar sa shima ya tada ya bi bayan ta. *MS Indabawa* [1/18, 14:36] Maryam S Indabawa🥰: LABARIN RAYUWAR* *ASMA'U HUSNAH* By *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers* Dedicated to *My Life. My momy* 76-80 *Manzon Allah(ﷺ)* Yana Cewa: *"Kuyi Aiki Domin Kowwa Ana Saukake shi ya Zuwa Abinda Aka Halicceshi Donshi ne"* (Bukhari da Muslim).* Ranar alhamis da wuri ta gama komai ta shirya tayi dakin Dady. Karfe takwas da arbain ta gama komai ta shiga dakin Yaya Buhari. Gaisawa sukai kawai ta fita duk dan kar ta makara. Shi kansa yau yasha mamakin ganin Asma'u bata tsaya jan magana ba. Baba ma da ya gama shiryawa ita kawai yake jira tana shiga ya tada mota suka nufi makaranta. Suna cikin tafiya motar ta tsaya. Fita Baba yayi Ya taba motar ya dawo amman shiru. Sai da yafita sau uku ana hudun Asma'u ta ce, "Baba me ya samu motar." Baba ya ce, "Asma'u kinsan ance karfen nasara bai da tabbas motar nan lafiya muku fito amman kinga ta tsaya taki tashi." Fitowa tayi ta duba agogo tara saura minti biyar. Waya Baba ya dauka ya kira mai gyara motocin gida ya fada masa inda yake Kallon sa Asma'u tayi ta ce, "Baba bari na hau napep dan na makara gashi zanyi submitting aasignment " "To bari na tsayar miki da Napep din.' "Aah Baba na gode." Ta fada tana dan matsawa. Mamaki take ganin karfe tara amman ji yan makaranta sai zirga zirga suke bama maza yan makarantun gwamnati. Duk Napep din da zai zo a cike yake zuwa. Wata Mota ce ta tsaya a gaban ta. Matsawa Asma'u tayi. Kara binta akai ta kuma matsawa. Fitowa yayi daga cikin motar. Wani hadaden saurayi ne ya fito. Fari ne, yana sanye da Ash kalar shadda kafar sa da bakin takalmi haka hannun sa daure da bakin agogo. Kansa bbabu hula sai gashi dake kwace luf luf. Yana da idanu, haka nan hancin sa dogone har baki. Karasawa yayi gun ta cikin nutsuwa ya ce, "Assalamu Alaikum." "Wa'aikulum salam!" Ta fada tana dan matsawa daga wajen. Kara bin ta yayi ya ce, "En mata ina zaki?" Ko kallon sa batai ba ta fara tsaida wani Napep. Bai tsaya ba sakomakon cikar da yake. "Naga kamar makaranta zaki kizo na rage miki hanya." Dagowa tayi ta watsa masa wani irin kallon sannan ta matsa wajen wani napep da ta tsayar. Kallon ta yayi har ta shige ciki sannan yayi murmushi ya shiga motar sa ya tafi. Tana zuwa ta tadda har an yi submitting ga wani malamin yana musu lacturrle. Kuka ta saka. tana zaune har lecturer ya fito. Ta shiga ajin ta kifa kanta a benci tana cigaba da kuka. Zainab ta matso gun ta tana bata hakuri sai ga. sir Sabir nan. A haka ya shigo har ya gama lecture Asma'u bata dago ba. Sai da zai fita ya dan matso gefen ta ya ce yana son ganin ta. Sannan ya tafi. Asma'u duk ta tsure dan tasan akan bai ga assignment din ta ba. "Zainab Allah bazani ba ni nagaji da kullum complain wallahi." "Kiyi hakuri kije baki san me zai faru ba." Da haka Zainab ta lallabata ta tafi office din nashi. Da sallama ta shiga bayan tai knocking an bata izinin shiga. Kai daga kallon ta ma zaka san ta sha kuka dan idon ta yayi ja dashi. Sir Sabir ne zaune a wata kujera sanye da Wata brown shadda. Gefen sa gayen da ta gani dazu a hanya ne yaso ya rage mata hanya. Waya taji Sir sabir yana yi yana cewa, "Ki nifa ban san ta ba a ranar nima na taba ganin ta." Shiru yayi sanna ya ce, "Sai kinzo. In kuma na fita ne shikenan." Ya kashe wayar. Kallon sa ya maida kanta ya ce, "Mene?" Kallon sa ta tsaya yi ta ce, "Uhmm uhmm!" Sai ku a tayi shiru. Fauwaz dake, gefen sa ya dago dan ganin da wa yake. Ido ya zaro ya ce "Kai kece?" Kallon sa tayi ta dauke kai ta ce, "Sir kace nazo." "Me yasa banga assignment dinki ba." Shiru tayi. Sai da ya kara nanata tambayar sannan ta dago ta kalle shi Fauwaz ne ya dago ya ce, "Friend ita ce wacce nake baka labarin na hadu da ita fa dazu. Motar suce ta lalace," Hararar sa Sabir yayi ya kalle ta ya ce, "Ke me yasa kullum kina da matsala ne, in tayi baki makara ba yau abu kaza ya faru me yasa ne *Husnah* " Fauwaz ya ce, "Haba aboki kayi hakuri man." Ya kalli Asma'u ya ce, "Beauty mene matsalar ki yanzu?" Banza tai masa tai kasa da kai idon ta na cikowa da kwalla dan ita da kai mata fada gara ka dake ta. Bata son fada a rayuwar ta yanzu zata fara kuka. Kallon ta Sabir yayi ya ce, "Mikon Assignment din naki kuma ki kara samun matsala na rashin submtting ko makara ki gani." Da sauri ta dauko ta mika masa. Ta ce, "Nagode!" Tayi hanyar fita da sauri Fauwaz ya mike zai bita Sabir yai saurin riko hannun sa. kafin ta bude kofa aka bude. Maryam ce ta shigo cikin shigar ta mai kyau ta saka doguwar rigar atamfa a mata dinkin mai dogon hannu. Mayafin ta dan yafa kai ba dan kwalli sai jaka dake kafadar ta. Tana ganin Asma'u ta saka dariya ta ce "lah Asma'u!" Sai kuma ta kama hannun ta. Ta kalli Sabir ta ce, "Uncle kace, baka santa ba a ranar ka taba ganin ta." Sai a lokacin Amsa'u ta tuno da statement din sa da ta shigo taji yana waya. Kamo hannun ta tayi suka shigo office din ta ce, "Ke nazo nema muyi sallama gobe zan koma garin mu gashi ban da number ki." Murmushi Amsa'u tayi wanda Fauwaz ya kasa dauke ido daga kallon ta. Hannun Maryam ta kama suka fita kallo Fauwaz da Sabir suka bisu da shi. Wajen Zainab suka karasa ta zauna sannan sukai musayar number sai hira ta balle. Dan har lecture tare suka shiga suka fito sukaje sallah sannan suka je cafteria suka ci abinci. Sai karfe biyar sannan suka rabu shima dan an tashi. Har bakin office din Sabir suka rakata suna daga mata hannu sannan suka juya. Sabir da ya zata ma ta tafi ta shiga ta zauna akan kujera ta ce, "Wash! Wallahi Uncle na gaji haka nima zan sha fama in na fara karatu." Kallon ta yayi ya ce "Daman baki tafi ba." Kai ta daga masa ta kalli Fauwaz ta ce, "Uncle Fauwaz ya kake?" "Ni ba ruwana da ke. Kin tafi kin barni." dariya tayi ta ce, "Ayi hakuri wallahi Uncle Fauwaz. Asma'u ce ta burge ni na dawo amsar number ta kasan gobe zamu shige." Kai ya daga ya ce, "Dan bani number na gani." "Tab ta ce, kar na bawa kowa wallahi." Sai lokacin Sabir ya ce, "In ba kwana zamuyi ba mu tashi mu tafi dare na yi biyar da rabi fa." Mikewa yayi ya dauki jakar sa da basket ya mikawa Maryam Amsa tayi suka fito tana ta basu labarin Amsa'u in ka kalli Sabir zaka zaci ba jin ta yake ba amman gaba daya hankalin sa na ga ita yana jin abubuwan da take fada. Da haka suka je gida haka tai ta bawa Mamah labarin Asma'u ranar dai har dare bata da magana sai Asma'u daga ta ce, tayi kaza sai ta ce tayi kaza. Ta ce, "Mamah baki ga ba yarinya karama ta na karanta medicine kuma a final year wallahi ta burge ni ga kokari da muka shiga lecture ita ke bada asma." Mamah ta ce, "Sai ki koyi da ita to." "Ai insha Allahu Mamah kuma nayi 'kawa." Shi dai yana zaune yana ji yana kara jin Asma'u na kara burge shi. Asma'u ma da taje gida sai da ta bawa Mami labarin yarinyar. Mami ta ce, "Daman haka rayuwa take wani na son ka wani kuma kin ka yake yanzu dai ita kince daga haduwa Allah ya sa mata son ki. To Allah ya bar mu ga masoyan mu." "Ameen!" Ta mike ta hau sama. Yaya Aslam ne ya kira ta bayan sun gaisa yake tambayar ta makaranta ita ma take tambayar sa wajen aiki. Soyayyar Asma'u da Aslam abin sha'awa ce da burge wa dan ba karamin son juna su suke ba kowa da son dan uwan sa son da basa son su taba rabuwa da junan su. Kowa na kula da tarairayar juna. Ga shi soyayyar su mai tsabta da kyau suke. *Haka rayuwa yake wani daya ganka yake jin son ka a zuciyar sa. Son Allah kenan wanda wani dabi'un ka su suka burge shi. Wani kuma halayar ka abubuwa da yawa dai. Allah ka bar mu da masoyan mu,* *Ameen!* Mutane na tambayata wai *Sabir* Mijina ne ko saurayi nane to daga *Sabir* har *Aslam* da *Fauwaz* all are my lovelly children. Really love then. *Husnah* kuma ina son sunan ne. *Masoya na nagode nagode Allah bar soyayya.* *Muje zuwa ga wani ya dadu a masoyan Asma'u shin ya kenan* *Ina mai bada hakuri na jina shiru da kukai jiya da night da na morning da ban ba. Nagode* *INDABAWA* [1/18, 14:36] Maryam S Indabawa🥰: LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Part *2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* *HAJOW* *Hakuri da juriya Online writer's* Dedicated to *My lovelly Mum* *81-85* Yau tin safe Zainab ke bugawa Asma'u kofa amman ko mostin ta bata ji ba. Abinda ya daga mata hankali kenan. Ta dau waya zata kira Buhari kenan sai taji shigowar sa. Da sauri ta karasa wajen sa ta na ce masa "Kaga Asma'u can kwana hudu taki bude daki yanzu na buga ma ko motsin ta bana ji." Da sauri yayi cikin gidan kofar yake duka amman sam ko motsi. Da gudu yayi dakin sa ya bude wata durowa ya dauko dayan key din Fita yayi da sauri yana budewa yaga ta kwance akan sallaya tana fitar da numfashi a hankali. Dago ta yayi yaga jkin ta duk a sake yake. Da gudu ya dauke ta ya nufi mota da ita. Asibiti yayi da ita da gudun gaske. kafin ya karasa ya kira Sabir ya fada masa gashi nan tare da Asma'u. Yana karasa wa aka kawo gado aka dauke ta kai aka yi wani daki da ita. Ruwa Sabir ya fara saka mata sannan ya fara duba mai ke damun ta. Ya gano har da rashin cin abinci sannan kuma jinin ta ya hau. Ya tabbata zuwan Aslam ne ya sata a wannan hali. Shi kan sa yasan Asma'u na mugun son Aslam. Dan ta sha fada masa. Sosai ya tausayawa mata dan ba karamin jin jiki take ba. Aslam dake can kwance shima ya ce da Mami yana son ya koma gida. Mami cewa tayi ya bari jikin sa ya kara kwari dan ko tafi sai da kyar yake taka kafar tashi. Rigima ya sawa Mami dole shi sai ya tafi. Da kyar ya bari ya kara kwana biyu, dan washe gari Buhari yana tafiya massalaci ya mike ya tafi gidan sa. Motar sa ya dauka ya dau hanyar Abuja, duk da jikin sa ba kwari. Tafiya yake yana tunanin halin da yake ciki. Wai shine zai rasa Asma'u. Hawaye ne ke zuba a idon sa. Dai dai zai shiga Abuja motar ya kwace daga hannun sa yayi cikin jeji. Asma'u kuwa tana kwance. jiki dai yaki yayiyu. Sam jiki ba samun sauki duk maganin da take sha. A gaskiya tasan tana kaunar Aslam kauna kuwa ba ta taba dainawa. Tana kwancen nan ba wanda take son ta gani inba Aslam ba. Kuka kam ita kadai tai tayi. Ta tabbata a yanzu tai rashin Aslam ba a da ba. Bikin ta da ya rage kwana biyar. Ba dan taji sauki ba aka bata sallama sai dan bikin ta da ya karato. Har gida aka kira akai mata maj lallai da gyaran kai. Rama kuwa ta kara ramewa tayi fari da ita. Ba abinda take iya ci. Da ta zauna ita kadai sai kuka. Zainab duk tai rabon katin bikin nata. Ita dai komai da akeyi nata ido ne. A bangaren Aslam kuwa Buhari na dawowa bai ga Aslam ba ya tafi gida. Motar sa yaga ya dauka nan da nan ya kira Momy ya sanar da ita Aslam ya taho. Haka ma ya kira ya sanar da Mami. Addu'a Mami tai masa Allah yakai sa lafiya. Momy kuwa tun karfe biyu take zuba idon ganin Aslam amman bata ganshi ba. Hankalin ta ne ya tashi. Can kuma sai ga sshi an kira ta da wayar sa wai yana asibiti. Asibitin taje a lokacin aka fito dashi daga emergency aka tafi dashi inda za'a bashi daki. Gun su tayi aka basu daki sannan likita ya kira ta. Bayanin abinda ya same shi yai mata cewar ya bugu ne sosai a bayan sa. Sai yan raunika da ya dan daddauje. Takardar magunguna ya bata ta amsa ta tafi ta bayar aka siyo mata. Lokacin da Momy ta buga waya tana fadawa Buhari abinda ya faru Suna tare da Sabir. Sosai Sabir ya tausaya masa. Haka su ka rabu jikin Sabir a sanyaye. Tunani kuwa har ya rasa wane iri zai yi. A ransa kuwa cewa yake yanzu yana ji yana gani zai raba farin cikin mutun biyu. Ya tabbata duk son juna su ke jefa su a halin da suke ciki. In har ya auri Asma'u yasan ya raba ta da farin cikin ta kuma Aslam ma bai da sauran farin ciki. Sai yanzu yake tunani anya da Aslam yana cikin haiyacin sa ya juyawa Asma'u baya Gaskiya da kamar wuya. Dan ya gano irin son da yake mata zai iya rasa rayuwar sa. Haka ya koma gida duk baida sukuni. A bangaren Aslam ma yana farkawa ya farai wa Momy kukan wai dan Allah ta taimaka a bashi Asma'u. Momy kam Mamaki ta dinga yi saboda sai da ta fada masa kar ya soma sawa ransa abinda ya riga da yai masa nisa. Da bata bashi amsa ba haka ya dinga kuka sai kace karamin yaro. Ganin numfashin sa na neman daukewa yasa ta ce, yayi hakuri za tai san yadda zatai. Duk da haka bai samu sukuni ba. shi dai ba wacce yake son gani sai Asma'u. Momy kam bata fadawa Mami abinda ya faru da Aslam ba. Kuma sai da ta hori Buhari da shima kada ya sanar da ita. Ita tunanin ta ma rashin zuwan ta bikin. Sai Allah yasa kuma ana jibi kamu aka sallamo Aslam daga asibiti. A gida ta barshi da Dady kan cewa jibi zata dawo. Haka Momy ta tafi tana tausayawa dan ta. Sai ta tuna lokacin da take cewa sai ya auri Asma'u amman yaki yac"e sai Preety zai aura amman shine har da suma gashi kuma yanzu ya dawo da son ta. Bangaren Su Mommah pretty kuwa ba karamin tashin hankali Ta shiga ba. Ganin Pretty har wata hudu ba ita ba labarin ta. Gashi ko waya bata yi nan fa suka hau bada cigiyar ta. Amman abin ko alamar nasara babu. Wata kanwar Mommah ce ta ce, a dage da addu'a Allah bayyana ta To An dauki wata ana ta addu'a da sadaka amman shiru. Da farko Mommah ma cewa tayi ita bata ga abinda addu'ar keyi ba. Kanwarta ce, ta ce, ai addu'a sai a hankali a cigaba da yi har Allah y amsa. Haka aka kara kaimi wata rana kamar daga sama sai ga pretty ta dawo da yaro a baya. Duk ta rame tayi baki sai wani wari take fitar wa. Tana ganin Mommahn ta tasa kuka. Ta fada jikin ta. Mommah ce ta daga ta tana toshe hanci, "Daga ina?" Ta tambaye ta. Pretty ta ce, "Mommah ruwa." Ruwa ta dauko ta bata ta kai ta bangaren ta ta ce tai wanka. Mommah ta rike ta ce, baza ta tafi ba dan tsoro take ji. Zama Mommah tayi ta shiga bandaki tai wanka. Tana fitowa tai wa dan ta wanka, Mommah ce tasa a kawo musu abinci. Nan aka cika dakin da abinci kala kala. Tin da ta fara cin abinci take turashi kamar wacce aka ce za a kwace mata. Mommah ce ta ce taci a hankali, amman ina haka yaron ta da bai fi wata biyu ba ta dinga cusa masa abinci. Tana gamawa suka zube a falo sai bacci. Ido Mommah ta zuba masu tana zubar da hawaye. Ganin yadda tayi baki, ta rame, ga yaro ko a ina ta samo shi. Bacci sosai tayi dan har akai magariba tana bacci. Sai da Dady ya dawo suka shiiga da Mommah ce ta same ta tana zaune, tana bawa danta nono. Tana ganin Dadyn ta ta mike. Dady ne ya karasa ya amshi yaron hannun ta. Magana yai mata amman da ta bude baki zata bashi amsa dai ta kasa magana. Har kuka tayi dan jin ta kasa magana. Dady na ganin haka ya samo malami yai masa bayani. Addu'a aka kara mikewa da ita da rokan Allah. Cikin hukuncin Allah sai ga Preety na magana. Anan ne take fadawa Dady duk abinda tayi da raba Aslam da Asma'u da bin malaman da take. Har da auren da sukai da boka wannan yaro kuma dan ta ne da boka, Bata taba zaton zata kubce daga wajen boka ba. Sai rana daya ta ganta ta samu hanya har ta fito. Bara tayi sannan ta samu na mota. Da kyar wata motar koso tumakai ta dauko ta. Acikin wajen da tunakrn suke ta zauna duk da wajen kashi da fitsarin su ne. Da haka suka karaso har kano aka sauke ta. Da kyar ta samu ta karaso Abuja. Take fada musu a kafa ta karaso gida. Jikin ta kuwa yayi wani iri kamar konuwa ga kaikayi. Asibiti Dady ya fara kkai ta amman ina abin ba na wasa bane. Da aka basu wasu gwaje gwaje aka gano tana dauke da cutar kanjamau. Dady sosai ya razana. Preety kuwa kuka ta dinga yi tana dana sanin abinda ya faru. Haka suka koma gida bayan an basu ranar da zasu na zuwa ganin likita da amsar magani. Sosai Pretty ta razana da rayuwar duniyar nan, Ganin yadda take da amman yanzu ji yadda ta koma. Ji dan da take riki dan shege, kuma ma na boka wai. Haka nan ita ce ke dauke da kanjamau, yanzu wa zai aure ta. Lallai *Duniya abar tsoro* *MS Indabawa* [1/18, 14:37] Maryam S Indabawa🥰: LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Part *2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* ?? *HAJOW* ?? *Hakuri da juriya Online writer's* Dedicated to *My lovelly Mum* *86-90* Yau ta kama kamu Asma'u ansha lalle da gyaran kai. Duk da a kwance take sosai dan yanzu haka ma wani irin ciwon kai da zazzabi ke damun ta. Tana kwance Zainab ta shigo da mai kwalliya ta ce, "Asma'u tashi mai kwalliyar tazo." Da kyar ta iya mikewa idon ta jajir ta shiga bayi. Kasa sakawa jikin ta ruwa tayi sboda sanyin da take ji. Fitowa tayi ta saka kayan da zata amfani dasu. zama tayi aka farai mata kwalliya. Yar kadan akai mata amman ba karamin kyau tayi ba. Ana cikin mata dauri Nusaiba ta kira ta. Dagawa tayi murya a sanyaye ta ce, "Amarya" Dariya Nusaiba tayi ta ce, "Amare dai. Ya kunyi kamun ne, nifa har na gama shiri fita kawai zanyi. Yanzu Uncle Sabir ya kira ni wai ya muka tsara dinner nace ai ni ke na barwa komai." "Uhmm kema dai. Ni ba wata dinner da zan yi. Yazo nan kawai." Nusaiba tace, "Ke kin isa ma. Kinji ana jira na bari naje mayi waya anjima." Ta katse wayar. Kallo ta bi wayar da shi ta ce, "Oh wai wannan ce kishiya ta. Ita sai murnar bikin take yi." Maryam ce ta kira ta. Ta ce, "Anty kiyi hakuri sai gobe zan taho yau zan tsaya wajen kamun Nusaiba. Jibi wai za ai dinner." Asma'u tace, "Nifa ba wata dinner da zanyi." Shiru Maryam tayi a ranta tana tunani ko Asma'u bata son a hada musu dinner su biyu ne. Sallama sukai tayi wajen Momyn ta tana fada mata gwara kowa yayi event din sa kar a wani hada. Haka kuwa akai dan Mamahn Sabir ma haka tace kowa yai nasa. A wajen Kamu kuwa Asma'u sai rawar sanyi take ga ciwon kai. Anyi hotuna da kawayen su da yan uwan Dady da Mami. Inda kafin a tashi jikin Asma'u yayi zafi kamar wuta. Nan da nan Momy tasa aka maida ita gida. Ciwo sosai ta kwanta. Washe gari akai Monday's even Amman Asma'u da kyar ta iya zuwa. Asabar dinner amma ranar a kwance sosai Asma'u take dan har asibiti aka tafi da ita. Riketa sukai suka bata gado ana mata karin ruwa. Dinner dai da ba ayi ba kenan. Rannar lahadi da safe aka daura auren Asma'u duk da tana asibiti lokaci nayi taji wata faduwar gaba. Kuka ta sawa Momy dake wajen ta. Momy sai lallashi take yi. Ba wanda yazo asibiti a ranar sai Zainab. Shima abinci ta kawo fuskar ta dauke da fara'a sai tsokanar Asma'u take wai ta kwanatr da hankalin ta ta samu abinda take so ta mike. Kiran da Mami ke mata yasa ta mike ta tafi ba tare da ta cigaba da tsokanar Asma'u ba. Asma'u kam zuciyar ta ta gama karaya ta rasa Yaa Aslam kenan. Da dare aka sallamo su gida suka nufa dan gidan ma har ya rage jama'a. Dakin ta aka kai ta. tana kwance akan gado duk ranta a bace. Zainab ce ta shigo ta ajiye roba sai karamin towel a gefe. Saboda jikin ta yai zafi za a fan sa mata ruwa. Kai ta dauke ta lumshe idon ta. can taji an bude dakin. A hanakli taji ana taciya har aka karaso bakkin gado. Bata san waye ba dan haka ta kara gyara kwanciyya. Roba taji an dauka an tsoma towel a ciki. Ji tayi an tada ta zaune, ana cire mata kayan dake jikin ta. Karamin wandon dake jikin ta kawai aka bari. Ido ta kara lumshewa. Saboda bata son bude su fan yadda suke mata zafi. Jin an soma goga mata towel ta ajiye wata uwar ajiyar zuciya. Ji tayi ana ta goga mata ruwa a jikin. Shiru tayi abu daya taji shine, an fi goga mata a kirjin ta. Duk da haka batai gigin bude ido ba. Can kuma sai taji kamar kamshin Yaa Aslam amman kuma sai ta tuna baya garin ma. jini shirun yai yawa yasa ta a bude idon ta a hankali. Waza ta gani? Yaa Aslam ta gani durkushe a gaban ta. Ido ta zaro ta mike da sauri. Murmushi ya saki. Bandaki ta shiga da gudu tana dafe da kirjin ta. Ta jima a bandakin tana kukan da ta rasa dalilin name ne. Sannan kuma tana mamakin taya Yaa Aslam ya shigo har ya ke shafa mata ruwa. Ta jima a bandakin tana kuka ita kadai dan har sai da taji Zainab ta shigo tana kiranta. Fitowa tayi daure da towel tana rawar sanyi. Dan wani zazzabi ne ya kara ta yar mata. Kayan bacci ta fito ta saka. Har ta kwanta Zainab ta ce, taje falo ana neman ta. Hijab ta dauka ta saka ta mike ta fita a hankali kirjin tane bugawa. Falo ta fito jiki a sanyaye dan wani zazzabi take kara ji. Kan ta kuwa kamar zai rabe gida biyu. Ta shiga falo taga Mami da Momy sai Uncle Habu (kanin Dady) sai Yaa Buhari da Sir Sabir. Taji dadi da bata Aslam a dakin ba. Dukkan su murmushi ne akan fuskar su sai hira suke. Kirjin ta ne ya buga ta ce, "Allah yasa ba cewa za'ai na fito mu tafi ba." Karasa wa falon tayi ta zauna a gefen Uncle Habu. Mutanen dakin ta gaisar daya bayan daya sukai mata sannu. Kasa tayi dakai. Uncle Habu ne yai gyaran murya ya ce, "Alhamdulilah Asma'u yau Allah ya nuna mana ranar Auren ki. Muna fatan zaki zama mace ta gari a wajen mijin ta. Kafin nan Asma'u. Asma'u duk abinda ya faru gareki ki dauka taki kalar Kaddara ce." Yai shiru, sannan ya ce, " Auren ki dai bai dauru da Sabir ba." Dagowa tai da sauri ta kalli Uncle Habu sannan ta kalli Sir Sabir. Murmushi ya sakar mata. Uncle Habu yacigaba da magana, "Yau a wajen daurin aure anzo daura auren ku Sabir ya dakatar ya ce, a daura auren ki da yayan ki Aslam." Nan ma da sauri Asma'u ta dago tana kallon Sabir tana girgiza kai. Murmushi ya sakar mata, yana mai girgiza mata kai ganin hawaye na shirin fitowa daga idon ta. Uncle ne ya cigaba da magana ya ce, "Ko da na tambaya akan me za'a fasa da shi sai ya kawon dalilan sa kamar haka:- Sabir ya ce, Uncle ina son Asma'u amman nafi son samuwar farin cikin ta. dole na hakura da ita tunda suna son juna su ita da Yaa Aslam. Dan ciwon da Aslam ya kwanta ma akan tane, haka ma kema kina son sa." Kai Asma'u ta fara girgizawa, Uncle yace, haka "Haka sabir yacigaba da bani dal'lan sa. Ya ce, Na yadda Yaa Aslam na son ta kuma in na aure ta mutum biyu zasu rasa farin cikin su. In ni na hakura ni kadai ne zan ji ba dadi kuma nima na lokaci ne tinda na samu wacce ke sona tsakani da Allah. Nagodewa Asma'u dan ita tai min wannan gatan bazan taba mantawa da ita ba. Ina son Asma'u amman na hakura da ita Allah bata zaman lafiya da mijin ta." Kukan da Asma'u take boyewa shine ya fito fili ta fashe da kuka. Zainab da shigowar ta kenan ta karaso tana lallashin ta. Uncle ya ce, "Ki daina kuka ki godewa Allah. Ina miki fatan Alheri Allah ya baki zaman lafiya. Ina farin ciki yau burin Yaya Suleiman ya cika. To Allah ya tabbatar da alheri. Ki kula da mijin ki. Allah miki Albarka." Ya mike ya fita. Mikewa Momy da Mami sukai suka fita. Haka ma Yaa Buhari ya mike ya fita, bin bayan sa Zainab tayi ya rage daga Asma'u sai Sabir. Mikewa yayi ya karaso gefen ta. Ya ce, "Haba Husunah mene na kuka. Ki godewa Allah da ya sa na gane irin son da Aslam yake miki na tabbata Aslam na kaunar ki fiye da yadda nake kaunar ki, akwai dalili mai karfi da ya hana shi auren ki a baya zai iya zama ko bayin kan sa bane." Dagowa tayi idon ta jajir kamar gauta ta ce, "Ni na fada maka yanzu ina son sane, bana son sa. Bana son sa sam. meyasa zakai min haka Sir. Yaa Aslam ba sona yake ba. Mutumin da yaki ni me ya dawo dashi gare ni......" Sai kuma ta fashe da kuka. Sabir ya ce, "A'ah Asma'u kar zuciyar ki ta dauki Aslam da wannan tunanin ki yadda da Aslam. Aslam na son ki. Aslam na kaunar ki, ni na yadda kuma nasan zaki ji dadi da Aslam amman dan Allah ki daina cewa bakya son sa. Nasan kema kina son sa. Ki amshi kaddara da Alalh ya saukar akan ku. Baki san me gaba zai faru ba. Nagode miki Asma'u da kika zaba min abokiyar rayuwa. Yau an kawo min Nusaiba daki na kuma duk a dalilin ki nagode." Ya mike ya fita. Kallo ta bishi da shi. Kuka ne ya kwace mata ta kifa kanta a kan kujera tana ta sharar kwalla. Da kyar ta mike tayi daki tana wani irin kuka. Kan ta kuwa ko ya ta motsa ji take kamar zai fashe dan azaba ko wuyanta bata son motsa shi. A haka Zainab ta same ta ta zata ma bacci take. Shirin kwanciyya tayi ta kwanta da danta. Can cikin dare Zazzabi ya tada Asma'u sai kuka take. A daren suka kara tafiya asibiti ba shiri. *MS Indabawa* [1/18, 14:37] Maryam S Indabawa🥰: LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 *Hakuri da Juriya Online writers Association * *Gidan Amanci da albarka* Dedicated to *My Lovelly Momy* *Mahaifiya ta abar alafahari na. Allah ya sa ki gama da duniya lafiya*zn 91-95 *Wani mutum yacewa Hasanul Basry:Ya Aba Sa'id ina kawo maka kukana akan 'Ke'kashewar zuciyata saiyace masa:Ka ladabtar da zuciyarka da ambaton Allah* Aslam ne ya shigo shima gefen Dady yayi shida Asma'u suka sa shi a tsakiya suna masa sannu da zuwa. Yaya Buhari ya ce, "Wallahi Mami a gidan nan ba a so na." Sai a lokacin Aslam ya kula da shi. Dariya yayi ya ce, "Aah 'kanina ashe ka dawo," Kai ya dauke wai yayi zuciya. Dariya sukayi. Asma'u tayi gefen sa ta ce, "Sannu bro ya aiki?" Banza yai mata. Kukan karya ta fashe dashi in kaji yadda ta fashe dashi kayi zaton na gaske ne. Nan da nan Yaya Buhari ya jata yana bata hakuri. Dariya ta saki ta ce, "Daman nace sai ka.kula ni." "Kai amman yarinyar nan kinga lago na." Ya fada yana daga ta daga jikin sa. Daga haka suka hau hira. Har karfe goma suna falo sannan Aslam da Asma'u suka tafi gun cin abinci. A can ma sun jima suna hira sannan suka ci abincin cikin so da kauna. Aslam ya ce, " *Husnah* ji nake ina ma anyi abin nan gidan mune mu sha soyayyar mu." "Lokaci dai. Allah nuna mana." "Ameen! Allah har na hango yadda zamuyi soyayya nake." "Kai Yaa Aslam! Kana son soyayya." "Dole naso ta *Husnah* dan wanda bai soyayya bai son dadin duniya nan ba soyayya tayi. Allah kuma ya bar mu da masoyan mu." "Ameen!" sannan suka mike suka koma daki. Sallama sukai wa su Dady kowa yayi dakin baccin sa. Duk abinda ta saba tayi sai da ta gama su sannan ta kwanta. A haka ma sai da suka kara yin waya kafin su kwanta. Sun jima suna waya sannan sukai sallama bayan sunyi alwala. Washe gari lahadi yini sukai tare. Ko gajiya da zama tare ko hira basa yi. Sai dai ka jiyo murmushin su ko kaji dariyar su. Mami dai bar musu falon tayi, haka suka yini a gidan. Tare suka ci abinci suka yini sallah ce ke daga su. Bayan sunyi sallahar la'asar, ne ya ce, Asma'u ta shirya ssu fita. Wanka ta shiga tayi, ta fito ta saka Wata doguwar riga fara an mata ado da jan stones sai Jan mayafi da jan cover shoe. Wata jar jaka ta dauka. Turare ta fesa ta fito tai dakin Mami. Mami na zaune tana kallo Asma'u ta shiga Kallon ta Mami tayi ta ce, "Sai ina kuma?" Murmushi Asma'u tayi ta ce, "Zan raka Yaa Aslam ne." "Toh! A dawo lafiya." "Allah yasa." Ta mike tayi waje. A kasa ta samu Ya Aslam ya na sanye da farin wando da jar riga. Takalmin kafa sa ma ja ne. Sai tashin kamshi yake yayi kyau. Yana ganin Asma'u yasaki murmushi ya ce, "Wow My baby tayi kyau munyi anko." Murmushi ta yi ta ce, "Ka fini yi." Wayar sa ya zaro ya ce, "Zo mu dau selfie." Gefen sa ta karasa ta tsaya matsowa yayi jikin ta, ya dauke su. Ya musu fin kala biyar sannan ya dinga daukar ta. "Yaa Aslam ya isa haka." Ta fada saboda taga ba alamar tsayawa. "To muje." Ya fada yana kamo hannun ta. Fita sukai ya karasa gun Baba ya amso key mota suka shiga. Shoprite suka shiga suka wuce cinema. kallo suka danyi sannan suka fito suka shiga ciki. Sun shiga suka nufi gun kayan sakawa. Sosai yake jidar mata dogayen riguna masu kyau da tsada. Haka ya nufi gun takalma da jakun kuna. Sosai ya kashe mata kudi sannan suka nufi gun alawa ya siya mata ice cream. Bayan anyi total ne aka dibi kayan akayi wajen mota dashi. Suna tafe suna hira taji ta bugi abu tayi baya zata fadi. Da sauri ya rikota ta fada jikinsa. Kafin ta dago taji Yaa Aslam ya dago ta yana cewa, "Ba dai matsala ko?" Kai ta daga masa, kamshin turaren da taa shaka shi yasa tai saurin dagowa. Ai kuwan shine, yana sanye da bakin wando da jar riga, yayi kyau sosai dashi. Ba kowa bane face Sir sabir. "Sorry!" ta furta a kasan leben ta. Yaa Aslam ne ya kama hannun ta suka bar wajen. Sabir kowa kallo yabi su dashi. Yana me lumshe idon sa. Suna fita ya ce, "Sannu Baby na ko na dauke ki ne." Kai ta girgiza ta ce, "A'ah nagode zan iya tafiya ai." A hankali suka karasa gefen Mota suka shiga suka bar wajen Suna zuwa gida ana kiran sallah isha'i Daki suka shige sukai sallah sannan suka sauko kasa. A kasa suka samu har Dady ya dawo. Saannu da zuwa sukai masa sannu da zuwa Abinci suka ci sannan suka koma falo ana hira. Sai karfe tara suka tafi makwancin su. Washe gari Monday. Tana gama abinda zatai ta shirya cikin wata pink kalar doguwar riga. Milk mayafi da takalmi ta saka. Sai pink kalar jaka. Batai kwalliya ba fuskar ta daga hoda sai man lebe. Wajen Dady taje. Tare suka karya. Sannan ta fito. Yaa Aslam ta gani a falon sama. Karasa wa tayi gun sa. Yana sanye da Bakin wando sai blue kalar riga mai dogon hannu. Yayi kyau sai tashin kamshi yake. "Yaya nah ina kwana?" Ta gaishe da shi tana zama a hannun kujerar da yake. "Lafiya lou. Ya Baby na ta tashi." Murmushi tayi ta ce, "Lafiya Alhamdulilah." Sannan ta mike ta sauka kasa. Basket din abincin sa ta dauko wanda ta zuba masa komai a fulas din sa. "Mu tafi?" Ya fada yana tambaya. Kai ta gyada masa, dakin Mami suka yi sukai mata sallama sannan suka wuce zasu sauka. Mantawa tai bata je gun Yaya Buhari ba. Wannan yasa tai ce "Ina zuwa!" Dakin yaa Buhari ta dosa, yana kwance ko alamar tashi bai yi ba. Kara tai masa a kunne da sauri ya mike a firgice. baya ta dan ja ta ce, "Ina kwana?" Ta fada tana ja da baya a hankali. Ganin ya mike yasa tai saurin fita a dakin tana dariya. Yaa Aslam dake tsaye yana jiran ta ya ga ta fito har ta sauka shima yabi bayan ta yana murmushi dan yasan tayi tsokanar da ta saba. A bakin mota ya ganta a tsaya budewa yayi ta shiga ya rufe sannan ya shiga bangaren sa. Tafiya suke a hankali suna hira abinsu. Har kofar department din su ya kai ta sannan ya kara mata kudi akan wanda Dady ya bata. Sallama yai mata ya ce, "Sai ya dawo daukar ta." Sai da ta ga tafiyar sa sannan ta nufi ajin daukar darasin su. Tana shiga taga Zainab zaune, karasawa tayi gun ta suka gaisa. Batai minti biyar da zuwa ba sai ga Sir Sabir nan ya shigo. Sanye yake da Milk din shadda ana mata aiki da milk din zare. Yayi kyau dashi. Kasa tayi da kanta tuna haduwar su jiya. Lectures yake musu da yayi tambaya zai yi pointing din ta. Tin tana jin kunya har ta sake tana bashi amsa. A haka suka gama lectures din. Da zai fita ya duka zai dauki wayar sa, yai mata magana a hankali cewar ta same shi a office. Wata faduwar gaba taji ta doke ta. A hankali ta daga kai ta kalle shi. Ita yake kalla saurin kawar da kan ta tayi tana wasa da yatsun ta. Waje ya fita. Wata ajiyar zuciya ta sauke, ita bata san hadin ta da malamin nan ba amman dai tana ji yana burge ta ko dan saukin kansa. Da kamar baza taje ba sai kuma ta ce da Zainab zataje ta dawo. Fita tayi ta nufi office din nashi jiki a sanyaye. Knocking tayi ya bata izinin shiga. Da sallama, ta shiga office din ta tsaya daga bakin kofa. Kallon sa tayi sau daya ta dauke idon ta. Yana zaune a kan kujera gaban sa, farfesun kifi ne da Doya da kwai. Kamshi ya cika office Din ci yake kamar baya son ci fuskar sa kuwa sai bata ta yake kamar mai cin magani. Kallonsa ya maida kan ta ya kasa dauke ido daga kallon ta. Yana son yarinyar nan amman bai san ta inda zai fara ba. Kawar da tunanin da yake yayi ya ce, "Zo nan!" Da kamar baza taje ba sai kuma ta dan matsa. Kallon ta ya kara yi ya rasa mene dalilin kiran nata. Kai ya dan shafa, ya ce, "Zo kici!" Kai ta girgiza ta ce, "Na koshi." Fuska ya bata, ya ce, "Zamu bata inda zan na baki abu kina kinci. Maza zo kici." Matsawa tayi ta zauna a kasa ba dan zata cin ba. Fulas din ya matsar mata dashi ya ce, "Bismillah!" Agogon hannun ta kalla sannan. Ta ce, "Zan je nayi Assignment fa." Ta yi maganar murya a shagwabe dan har ga Allah ta riga da ta saba da shagwaba in tana abu. bama in tana bukatar abu. Sabir kuwa jin muryar da take magana da ita yasa nan da nan tsigar jikin sa ta mike. *INDABAWA* [1/18, 14:38] Maryam S Indabawa🥰: LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Part *2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* ?? *HAJOW* ?? Dedicated to *My lovelly Mum* *96-100* Kina Ina Fateema kibiya. A gaakiya ina yaba hankalin ki. Da kokarin ki. Allah ubangiji ya kara basira da zakin hannu ni Maryam ina son ki Mikewa yayi ya durkusa a gaban ta. Hannun sa ya daura a kan cinyar ta Da sauri ta bude idon ta. Kallon sa ta tsaya yi kamar yadda shima ya kasa dauke idon sa daga kallon ta. Hannun ta ya kamo ya fara murzawa a hankali. Ya kira sunan ta a hankali. Ya ce, "Husnah ki yadda dani wallahi ina son ki. Duk abunda ya faru ki manta da shi." Ido ta rufe dan ita ta kasa mantawa da abinda Yaa Aslam yai mata. To wai mema tai masa da har ya guje ta bayan yasan bazata ta iya rayuwa ba shi ba. Bayan yasan duk farin cikin ta yana gare sa. Bayan yasan shine ruhinta. Shine sirin ta daga mahaifinta sai Mami sai Shi da Yaa Buhari sune kadai gatan ta. Amman shine ya juya mata baya. Ko yasan halin da ta shiga. Ko yasan irin jinyar da tasha. Ko yasan irin azabar da take sha a duk sanda lokacin kiran sa ko turo mata da sako yai bai turo mata ba. Duk shekarun nan da suka wuce in dai zata kwanata bacci sai tai kuka. Dan ya riga da ya sabar mata shine mutun na karshe da yake saka ta bacci da kishoshin Annabawa da sahanabai. Amman duk a lokaci daya ya rushe duk abinda ke tsakanin su. Tabbas ya dawo gareta ne dan ya raina mata hankali. Ina dayar matar tasa. Ya dawo gare ta ne dan yasan irin son da take masa. Ya dawo gare ta ne dan yasan da shi kadai zata iya rayuwar aure. Ya dawo gare ta ne dan yasan duk lagon da zai amshi zuciyar ta. Ya dawo gare ta ne dan yasan irin son da take masa. To yayi karya duk son da take masa baza taba sakar masa ba. Inda da ya nuna baya sona nima yanzu na hakura da shi. Zan zauna da koma waye amman banda da Yaa Aslam. Bazan zauna dashi ba Yaa Aslam ya wahalar da ni. Tana tuna irin hirar rakin su da yakan ce bazai taba rabuwa da ita ba. A lokacin in ta kawo misalin abinda zai iya raba su har haushi yake ji. Amman lokaci daya ya rabu da ita. Ta kan tina irin alkawarin da yake mata da irin son da yake mata to duk suna ina. Lallai in ta kara yadda da Yaa Aslam zai kara yaudarar ta ne. Tasan tana son Yaa Aslam amman zata danne zuciyar ta ta nuna masa ita yanzu ba son sa take ba. Sai ta kwatar wa kanta yanci a gun sa. Idon ta ta bude jajir da su. Aslam dake rike da hannun ta ya zuba mata ido ya kara bude idon sa ganin yadda idon ta ya kada yai jajir. Kuka ta fashe masa da shi. Nan da nan ya hau lallashi amman sam taki yin shiru. Sai da kyar ta yi shiru nan ma ta mike ta yi cikin gida tana sharar hawaye. Mami dake falo ta ga wucewar ta. Kai kawai ta girgiza. Dan tasan Asma'u na son Aslam. Tana lura da yadda take rufe daki kuma duk tasan akan sa ne. To ai dai jikin ta yai sauki dan haka tazo su shirya su tafi dan ta fara tausayawa Aslam. Bama da tasan kafiyar ta. Tana zaune Aslam ya shigo shima duk yanayin sa ya sauya. Kallon sa Mami tayi ta ce, "Ya dai?" Kai ya dan sosa ya ce, "Ba komai!" Mami ta ce, "Shikenan ka fara shirin tafiyar ku. Tinda jikin nata yai sauki nan da jibi sai ku tafi ko?" "To Mami Allah kaimu." Ya fada yana mikewa. Sama ya hau Mami ta bisa da kallo. Asma'u ta shiga daki ta shiga bandaki ta watsa ruwa tai alwala. Tana fitowa ta shafa mai tai salla. Tana kan sallaya Mami ta shiga dakin da sallama. Dagowa tayi ta amsa tana gyara zama. Zama Mami tayi agefen gadon ta ta ce, "Asma"u jikin ki yai sauki dan haka ki hada kayan ki nan da jibi sai ku tafi ko?" Wata faduwar gaba ce ta zowa Asma'u dan har sai da ta dafe kirji jin kamar zai fadi. Dagowa tayi ta ce, "Mami Allah da saura na." Mami ta ce, "Asma'u ba inda yafi dakin mijin ki dadi da gatan ki. Ki tafi ke karasa warke acan. Allah baki lafiya. Allah miki albarka." Kuka Asma'u ta saka ta ce, "Mami bana son na tafi na barki. Mami na rasa Dady kema kada na rasa ki Mami ni a nan zan zauna." Murmushi Mami rayi ta ce, "Haba Husnan Dady. Kinsan sai kwana yayi ake tafiya. Kuma kinsan Dadyn ki bai da wani buri da ya wuce ya ganki a gidan Yayan ki matsayin matar aure. To ki daure ko dan Dadyn ki ki zauna lafiya a gidan mijin ki. ni kuma ki kwantar da hankalin ki zan na zuwa ganin ki akai akai. Kuma ga Yaa Fati nan ma. Ki daina kuka in ba so kike hankali na ya tashi ba." Da sauri ta hau goge hawayen fuskar ta. Bangaren Sabir da Nusaiba kuwa zaman lafiya suke sosai take kula da shi shima kuma so sai yake kula da ita. Sai a yanzu yake jin son ta sosai a cikin jikin sa. Perty kuwa tana can ta koma ga Allah yanzu Aslam take so ta gani ta roki gafarar sa Tasan taci zalin Asma'u dan tasan soyayyar dake tsakanin su amman ta raba su. Dole ta nemo Asma'u itama ta nemi gafarar ta wannan dalilin ne yasa ta tafi kano dan neman inda Asma'u take. Har gida Zainab ta zo jin Asma'u zata tafi. Kayan gyaran jiki ta hado mata sosai, inda ta bata wasu ta ce ta tafi da su. Haka ma Maimuna har gida tazo tai mata sallama. Ana gobe zasu tafi suka je gidan Sabir. Gida ne mai kyau wanda aka zuba masa kayan more rayuwa kala kala. Tinda suka je Nusiaba sai nan nan take da Asma'u duk Asma'u ta kasa sakin jiki saboda kallon da Aslam yake tsare ta dashi. Shi yana mamakin Asma'u kamar ba ita ba. Duk ta canja masa. Anya kuwa Asma'un sa ce wannan. Shifa ko a gida baya ganin ta. Bare ya samu damar mata magana To in ya ganta ma ya samu fuskar magana man. Haka suka dan zauna sanna suka tafi gidan Mamah mahaifiyar Sabir. Sosai Mamah tai mata nasihar zama da miji sanna ita ma ta hado mata kaya ta bata. Gidan su Zainab suka je tayi wa mahaifiyar Zainab sallama. Daga nan kuma suka koma gida Duk tafiyar nan da suke kallo ne kawai nashi amman ya kasa koda mata magana. A haka suka karasa gida ta debo kayan ta ta shige. Sama ta hau ta ga Mami ta fito da akwati nan ta da na wajen Yaa Aslam da na wajen Sir Sabir da ya ce ya bar mata. Zama Asma'u tayi ta ce, "Mami na gaji. Sai kace ban saba fita ba." Mami ta dago ta kalle ta ce, "Kinsan jikin naki ne. Ya kamata kije asibiti yau." "Eh sai anjima zan leka." Asma'u ta fada dai dai shigowar Sabir. Mami ta kalle shi ta ce, "Kaga masu dibar kaya a kasa ko?" Kai ya gyada, Mami ta ce, "Kaje kace su zo so dauki kayan an gama." Mikewa yayi ya fita. Mami ta ce, "Tinda kince ke sai kayan Dady gasu can an saka miki su a mota." Murmushi Asma'u tayi ta ce "Mami ba haka bane, kinga Dady dan kar ya daurawa kowa nauyi ya siyon kayan nan. Kuma kayan nan da kyan su, bayan haka masu tsada ne to me za a canja ayi dasu. Kuma naga su aje yayi Mami dan zaman duniya dai kawai wani ma neman wanda bai kai shi ba yake amman bai samu ba." "Haka ne! Kayan na da kyau masha Allah." Mami ta fada. Suna zaune aka shigo aka kwashe duk kayan. Sai a lokacin jikin Asma'u yai sanyi ganin da gaske dai tafiya zatai. Daki ta mike ta shiga. Daren ranar tare suka kwama da Mami tana tai mata nasiha akan aure. Asma'u ji take kmar tace ta fasa. Wwai da da bata da burin sai ta ganta a gidan Yaa aalma amman yanzu duk bata so Washe gari da safe Mami da kanta ta hada mata ruwan wanka. Tai wanka ta shirya cikin wata Farar atamfa wacce akai mata adon da ja da baki. Simple make up tayi, ta saka jan mayafi da jan takalmi sai bakar jaka. Sosai tayi kyau. Ba abinda tta dauka saboda komai nata an tafi mata dashi. A falon sama ta samu Mami da Yaa Aslam wanda ya saka wata milk din shadda tai masa kyau. Sai tashin kamshi yake yi. Yaa Buhari a gefen sa. Sai Zainab dake dakin Mami. Gefen Mami tayi ta zauna. Yaa Buhari ya kalle ta ya ce, "Ji 'ya Malama tashi zakiyi dan yanzu zaku tafi." Baki ta turo ta dan harare shi. Daga kan da zatai sai taga Yaa Aslam ya zuba mata ido baki da hanci yana kallon ta. Kai ta dauke ta kalli Mami ta ce, "Mami ni kam in nace na fasa ai ya fasu ko?" Kai Mami ta daga. Yaa Buhari yai dariya ya ce, "Karya kike wallahi." Mami ta ce, "Ku tashi ku tafi." Kwanciyya tayi akan kafar Mami. Zainab ta fito ta ce, "A'ah me zan gani!" Yaa Buhari ya ce, "Eh man wallahi aka zan fitar da ke." Mikewa tayi ta fara zubar da hawaye. Murmushi Mami tayi ta ce, "To mene na kuka. Haba Husnahn Dady ki daina kuka bayan ga Momyn ki can tana jiran zuwan ki." Kai tai kasa da shi amman hawaye ya kasa daina zuba. Yaa Aslam kuwa kukan da take ji yake kamar yai me dan sam baya son kukan Asma'u. Zainab ce ta kama ta ta ce, "Haba Asma'u ki daina mana." Suka mike suka fita har da mami ta raka su compound sannan ta dawo. Asma'u kuwa sai jikin ta ya kara sanyi na jin rabuwa dai zatai da gida Sai da suka fita daga gida Aslam yaji Asma'u na kuka. Motar yasa Buhari ya tsayar sannan ya koma gidan baya. Jikin sa ya jata yana lalashi ta a hankali a hankali. Sannu a hankali tayi shiru. Tana rasa dalilin da yasa in har tana tare da Yaa Aslan take jindadi a ranta. Ko taji ta samu relief. A haka suka karasa airport ba tare da sun san anje ba. Har sai da su Yaa Buhari suka fita sannan yai musu knocking. Dogowa sukai yai musu nuni da waje. Jikin ta ta kwace daga nashi ta fita da sauri. Jakar ta ya dauka ya fita yana murmushi. Suna zuwa aka fara kiran su. Ba jima ba suka tashi. Asma'u na hawaye dan sai Yaa Aslam ne ya tallabe ta yana lallashi har suka shiga jirgi. A cikin jirgin ma jugum tayi tana kwance a kan kafadar sa. Suna sauka har motar gida tazo daukar su. Gida sukai. Asma'u duk sai taga gidan ya canja da ta jima bata je ba. Ba kamar da da ta samu hutu taje ba. Amman yanzu a kalla tai shekara biyu zuwa uku ba tazo ba. Suna fitowa Momy ta fito ta kama ta. Cikin gidan ta shige da ita aka bar Aslam da daukar jaka. Sama ta nufa da ita tana. Dakin guda aka kai ta. Ruwan wanka Momy ta hada mata sannan ta sauka. Bandaki ta shiga. Kafin ta fito an jere mata kayan abinci. Mai ta shafa ta saka wata bakar doguwar riga da ta gani akan gado. Sallah tayi tana zaune akan sallaya ya shigo dakin. Dagowa tayi ta kalle shi ta dauke kai. Sanye yake da wando three quarter daga alamu shima wankan yayi. A gaban faranti da aka jero mata abinci ya zauna. Ya ce, "Bismillah" Kai ta girgiza ta ce, "Alhmdlh" Murmushi yayi ya ce, "Humm! Ai gwara ma kici domin nasan baki ci komai ba duk yinin yau ga idanunki duk sun kumbura saboda kuka" Fuska ta bata ta ce, "Wa kuma yace maka banci abunci ba"? Kusa da ita ya matsa daf ya d'ora tsinin dogon hancinshi akan nata. Ajiyan zuciya ya sauke. Yana kallon ta ido cikin ido yace, "Nasan Husnah d'ita fiye da yanda take zato. Idan tana fad'amin gaskiya ina ganewa idan kuma tana fad'amin karya ma ina ganewa. Dan haka kina sanin abinda zaki fada min. Oya So let's eat, drink and....." Bai karasa fadar abinda xai fada ba ta ce, "Me?" Bai bata amsa ba sai kiss da yai mata a kumatu. Harshenta ta fito dashi a waje. Ai kam Charaf Yaa Aslam yasashi a baki. D'an kokarin tureshi ta farayi ganin ya fara sarrafata yasa tai la'asar. Har cikin kwanyar kanta take jin kiss din da yakeyi mata. Sai daya gama da kanshi ya d'an ja da baya kad'an. Kallon ta yayi da idon sa da sukai jajir ya ce, "Now let's eat" Asma'u da jikin ta yai sanyi sosai tai kasa da Kanta ta dauki cokali ta fara cin abincin a hankali. Kallon ta ya tsaya yi. Sannan ya bude dayan fulas din naman kazan ne a ciki. daukowa yyai ya mika mata. Amsa tayi tana ciki a hankali duk jikin ta a sake. Lemo ya mik'a mata, cikin sanyin murya tace "Na koshi." Cup d'in yai gefen bakin ta da shi. karba tayi ta kai bakin ta ta sha kad'an ta janye ta maida ta aje. "Duka zaki shanye" Yaa Aslam ya fad'a yana murmushi. Hararar sa tayi ta ce, "Haba dan Allah ni ina zan iya shanye wannan? Wallahi na koshi." Aslam yai murmushi ya ce, "Kokartawa xakiyi ko in maki d'ore kamar yadda da nake miki." Kai ta dauke, tana hararra sa ta kasan ido. Yau Kwata kwata sai take jin Yaa Aslam ya koma mata wani sabo daban. Ga shi tana kasa hana shi duk abinda yake mata. Ba yanda ta iya illa ta sha kamar yanda yake so. Shima kai ya kafa yasha nashi. Tashi yayi ba tare dayace mata komai ba ya fara cire rigarshi. Idanu ta zubawa kirjinshi da kwanjunan hannunshi. Murmushi Yaa Aslam yayi ya nufi wajen ta. Duk'awa yayi da niyar daukar ta. Ta mike za tayi waje. Kamota yayi ya dauketa ya direta kan gadon ya kura mata idanu. Cikin sanyin murya yace "Kina sona Husnah?" Banza tai masa kamar ba da ita yake ba. Murmushi yayi, ya zura hannun shi ta cikin rigar ta yai kark'ashin bayanta. Sannu a hankali ya fara d'age mata rigar jikin ta. Tana jinshi tai lamo kaman wadda batada rai. Kirjin ta sai dukkan uku uku yake Tana son ta hana shi amman ta kasa. Fuskan shi ya d'aura a kan nata ya fara gogo mata hancinshi. A hankali ya tallabota ya fara cire mata rigan. Tsotsan kunne ya fara yimata cikin natsuwa yana hura mata iska a ciki. Jin sanyin AC na ratsata ta ko ina na jikinta yasa ta farga batada riga. Jawo Hijab din ta tayi ta rufe kirjinta. Ajiyan zuciya Aslan ya sauke. Kara matseta yayi da kirjinshi sosai. yana shafa bayanta a hankali hadi da mazaunanta. Sanin zata iya guduwa a ko da yaushe yasa ya kara matsa ta a jikin sa. Hannu ya d'ora akan gashin ta ya 'dago fuskanta ya kaimata sumba a wuya, lips d'inshi ya tura cikin bakin ta a hankali ya fara tsotsawa yana zare bra dinta... Hannunshi ta rike gam. Chaan kuma ta saki ta zubawa sarautar Allah ido... Tasan ita halak dinsa ce to amman kuma tana tuna abunda yai mata. Tana can tunani taji ya fara wasa da ita sosai da sosai. Sosai jikin ta ya fara rawa, Duk sun fita a cikin hayyacinsu daga ita har shi. Hannun sa ta rike tana girgiza masa kanta. Ta ce "Dan Allah ka daina Yaa Asl......" "Shhhhhhhhhhh. Enough" ya fad'a yana k'ank'antar da murya chan k'asa 'kasa. Fuskantar ta juyar saboda ya matse ta ba damar tashi. ta fashe da wani irin kuka. Kuka sosai takeyi. Ganin ya kasa shawo kanta yasa Aslam sakin ta yana maida numfashi yana ajiyan zuciya. Da sauri ta mike ta saka kayan ta ta fice da sauri. Yana kallon ta ya saki ajiyar zuciya ya gyara kwanciyya. Tabbas yasan da duk abinda ya faru bai faru ba da yanzu yaga jinin sa a tare da Asma'u. To amman ji yadda Asma'u ke gudun sa kamar dodo. Asma'u da inda yaje gida suke tare kullum amman yanzu sai dai daga nesa. Har gara yau ma ya samu damar zama kusa da ita har ya umarce abu tayi. Yana son Asma'u so bana wasa ba. Amman ya rasa ta yadda zai nusar da ita ta yadda. Asma'u na fita tayi dakin Momy, Momy na zaune suna waya da Mami tana fada musu sun sauka lafiya. Asma'u na shiga ta ce, "Ga ta nan ma." Ta mika mata wayar. Gaisawa sukai tai musu ya hanya. Kan gadon Momy ta hau. Momy ta kalle ta ta ce, "Kinci abincin ne?" "Eh naci." Momy ta ce, "Me kike bukata?" "Ba komai!" "To kwanta ki huta." Ta kwanta. *MS Indabawa* [1/18, 14:39] Maryam S Indabawa🥰: LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Part *2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 Dedicated to *My lovelly Mum* *101-105* Yau kwanan su biyu a gidan Momy amman zai iya cewa rabon sa da Asma'u tin ranar da suka zo. Kullum tana daki a rufe bata fitowa falo ko da fito da ta ji shi take komawa. Ya zuba ido yaga Momy ta ce, su koma gidan su amman Momy tayi shiru. Haka ne yasa aka je aka share gidan a goge dan ya kagu ya tare. Momy kuwa tana can tana shirya musu walima da za'ayi ne kafin su tare tinda ba wani biki akai ba. Yau ya cire kunya ya ce zai fadawa Momy shi ta bashi Asma'u su tare. Yana shigowa ya same ta akan kujera tana duba wasu takardu. Yana zama ta mika masa wasu takardun. Amsa yayi yana dubawa. Dagowa yayi yana kallon ta. Murmushi tai masa ta ce, "Eh ai dole a hada maka walima Allah yayi Asma'u matar ka ce." Murmushi yayi ya koma gefen Momy ya kama hannun ta sai hawaye. Kallon sa tayi ta girgiza masa kai. Ta ce, "Mene na kuka?" "Dole nai kuka Momy. Momy kina sona Allah ya biya miki bukatun Alheri Allah yasa ki kyakyawan karshe." "Ameen! Duk wannan addu'ar ta mece?" "Momy kina sona da Asma'u kiga lokacin da nace bana son ta ke kika ce A'ah amman na ki sam. Wallahi Momy ban san me ya raba ni da Asma'u ba dan ban taba jin kin ta ba. Kullum da ita nake kwana nake tasho. Ina son Asma'u Momy." Asma'u da fitowar ta kenan taji yana maganar tai saurin komawa daki. Ajiyar zuciya ta sauke sai kuma ga hawaye nan ta rasa hawayen me take yi. Momy kuwa, hawayen sa ta share masa ta ce, "Ai Allah zaka godewa da yada Asma'u taka ce, gashi har ka mallake ta." "Haka ne Momy ina gode masa a ko da yaushe. Kuma ina gode muku." Ya mike ya ce, "Bari naje na fara rabo." Momy ta ce, "A'ah sai na ji ta bakin ta tana son naka ne har yanzu ko aah." Dariya yayi Ya fice, yana cewa, "Momy tsokana" dariya Momy tayi dan a duniya tana son dan nan mata daya guda tilo. Duk farin cikin sa shi take fata. Abinda ta dade bata gani a tare da shi ga shi yanzu ya dawo kullum farin ciki da annushuwa ne dauke a fuskar sa. Tasan duk wannan bazai rasa nasaba da samun Asma'u da yayi bane. Mikewa tayi ta yi sama. Dakin da Asma'u ta shiga. A kwance ta same ta. Mikewa tayi tana gyara zama. Zama tayi a gefen ta. Ta ce, "Asma'u kina son Aslam har yanxu ne?" Shiru Asma'u tayi a aranta ta ce ko bana son Aslam ai ba zan taba fada miki ba Momy bare ina son sa. Momy ta ce, "Karkiji komai ki fada min." Kasa tayi da kai ta daga mata kai, murmushi Momy tayi, ta mika mata katin hannun ta. Amsa tayi ta kalla. Murmushi tayi dan tasan Momy na son ta. Dagowa tayi ta ce, "Momy har wata hidima za'a kara." Kai Momy ta gyada ta ce, "Auren da muka dade muna fata ba dole ba. Yau Allah ya nuna mana kowa yaxo ya taya ni farin ciki na hada 'dana da 'ya ta aure." Murmushi Asma'u tayi tai kasa da kai. Wai yanxu Momy sirikar tace. Washe gari Aslam yai tafiya dan ya ce, shi zai je ya yo musu order kayan da zasu saka. Tin ranar Asma'u bata kara ganin Aslam ba, kuma bata neme shi ba. Shi kuwa yana can yana fama da rashin ta. Duk yadda yaso ya ji muryar ta baya samu, dan ko Momy ya kira ya ce a hada su da ta amsa bata magana wani lokacin ma kashewa take. Murmushi yake dan shi, yasan yai wa Asma'u ba dai dai ba. Amman bari zai wanke laifin sa ne bari da su tare. Cikin kwana biyu aka kara yiwa Asma'u gyara inda akai mata lalle da gyaran kai. Sosai tayi kyau ta koma amaryar tata dai. Yau ce ranar walimar da Momy ta hada a yau kuma zata tare a gidan ta. Har su Zainab suna hanya, ita da Mami da Yaa Buhari. Asma'u na ganin su ta rumgume su. Sai murmushi take. Dakin ta ta ja Zainab tana dauke da Dadyn ta. Tunda su zainab suka je take kallon ta ta ce, "Ke Asma'u wannan kyan fa tin kafin ki tare ko dai har anyi wani abu ne." Duka Asma'u ta kai mata ta ce, "Ai shi ba ruwan da.' Dariya Zainab tayi ta ce, "Ma gani dai." A ranar Yaa Aslam shima ya dira da kayan da ya taho masu da shi. Yana ganin Buhari ya yi wajen sa, ya fe, "Bro har kun zo." "Eh man kun taso mu." murmushi yayi ya ce, "Wallahi Momy ce." Suka shiga ciki yana daukar akwatin hannun sa. Dakin sa suka nufa shima. Karfe hudu har an gamai mata kwalliya. Kyan da Asma'u tayi ba zai fadu ba. Amman tayi kyau sosai. Ta saka wani Material Milk kala wanda akai mata ado da dark brown din material. Ta dauki dark brown din takalmi da jaka, da mayafi. Ta saka milk din fashion. Ruwan turare akai ma. Tayi kyau kamar ka sace ka gudu. Kowa yayi kwalliyar sa cikin shiga mai kyau. Dan lokacin ma har Maryam ta zo ita ma. Da yake a harabar gidan Momy za'ai har wajen ya cika da jama'a Bangaren mata daban na maza ma daban. Momy da kanta ta shiga dakin da aka shirya Asma'u ta kamo ta. A falon da ta zaunar da ita. Aslam ta kira ya fito shima cikin wata milk shadda da akai mata aiki da dark brown din zare. A takaice dai anko sukai kuma sosai sukai kyau. Tinda ya fito ya daura idon sa akan Asma'u ya kasa daukewa. Sai da Momy tai masa magana sannan ya kalle ta yana sosa keya. Hannun Asma'u ta kama ta kamo hannun sa suka sauka kasa. Mami dake zaune a kasa tana ganin su ita ma ta mike. Momy da Mami su suka fitar da yayan su. Har wajen zaman su suka kai su. Akai hotuna da kowa da kowa sannan aka ci aka koshi akai musu addu'ar zaman lafiya. Duk wanda yaga Aslam da Asma'u yasan sun dace da juna. Dan suna kusan dibar kamanni da sai shi fari ne tas. Ana kiran magariba aka tashi daga taron kowa yai cikin gida maza suka tafi massalaci dan da anyi isha'i za'a kai amarya gidan ta. Suna shiga ta shige toilet dan yin alwala amman sai ta ga ba hali dan period din ta yazo. Wanka kawai tayi ta fito. Momy ce ta shigo ta ce, tai sallah ga wani ruwan turare nan tai wanka dashi. Da toh ta amsa mata kawai. Bayan mintina kadan Momy ta dawo dakin. Ruwan wanka ta hada mata da wani hadin turare, mikewa Asma'u tayi tai wanka. Tana fitowa Momy ta kawo mata garwashi da wani turaren ta turarre jikin ta. Wani hadin humra Momy ta kawo mata da wata atamfa ruwan ganye da ruwan daurawa. Simple make up akai mata. Aka saka mata alkebba Golding kala. Momy tai mata ruwan turare sannan ta saukar da ita wajen kawayen ta da Mami. Nasiha sukai mata da addu'ar zaman lafiya. Sannan mutum biyu daga kawayen Momy suka fito da ita. Dakin Dady suka kai ta shima nasiha yai mata mai ratsa jiki. Sosai Asma'u take kuka dan sai yanzu ta san tayi aure. Daga nan suka tafi da ita gidan mijin ta. Sai Zainab dake can tana kintsa gidan. Gida ne katon gaske dan harabar gidan kanta katuwa ce, banda bayan gidan. Garden da swimming pool ne sai bishiyun kayan marmaru kala kala. Da lilo. Harabar gidan an kawata ta da fulawoyi. Kofa daya ce zata sada ka da shiga cikin gida. Da ka shiga kuma zaka ga katon falo aka saka masa wasu royal furnitures Coffee kala da adon milk. Haka ma labulayen kofi da milk ne. Daga gefen sa yar stair ce da wajen daining da kitchen. Kitchen din ta an cika mata da kayan amfani zamani. An mata adon sa irin na, Island kitchen plan akai. Daga can bangaren kuma Toilet ne. Sai kofofi biyu dake kallon juna. dayar tana dauke da falo, da bedroom guda biyu. Ko wanne an zuba masa kaya masu kyau da tsada. Daki daya akai masa adon pink dayan kuma aka zuba masasa irin kayan Babban falo. Kamar yadda falon ta ma adon pink din akai mata Dayar kofar ma, yar barende ce wacce zata fito dakai harabar tsakar gidan. Sai bandaki da falo da dakin bacci. Wannan shine bangaren mai gida Aslam, sai arabi'an cusin da aka saka masa red nd white. Haka ma bedroom din an zuba masa red an white kaya. Kayan kallo da kayan electronic duk masu kyau da tsada aka zuba su Gida sai sanyin AC da kamshin turaren wuta da yake. Kowa ya je yaga gidan sai ya sanya albarka da addu'ar zamab lafiya. Haka suka ajiye Asma'u a dakin ta, suka karai mata nasiha sannan suka mike suka tafi. Zainab ce kadai a wajen ta, Asma'u kuwa har lokacin in banda kuka ba abinda take. Jin kan ta take kamar zai fadi dan ciwo. Zainab ce ta zauna a gefen ta, ta kamo hannun ta. Dagowa tayi da idon ta jajir sai ta fada jikin Zainab tana kuka. Lallashin ta Zainab take tana cewa, "Haba Sis mene na kukan? Dan Allah kiyi hakuri ki daina." Shiru Awma'u tayi tana ajiyar zuciya. Zainab bata dade ba Yaa Buhari yai mata waya ta fito su tafi dan ya ajiye Aslam. Kara kimtsa ta tayi, sannan ta mike tana mata sallama. Tana fita Aslam ya shigo bayan sun yi sallama da Zainab. Kofa ya rufe ya shigo dakin da Asma'u take. A ciki ta amsa sallamar tana me dukar da kanta kasa. A gefen gadon ya zauna. Fuskar ta ya yaye, yana kallon fusakar ta da tai jawur da ita. Hannun sa ya saka ya janyo ta jikin sa, wata nannauyar ajiyar zuciya ya sauke. "Ina kaunar ki Asma'u ina kaunar ki Asma'u " Ya fada cikin wata irin murya. Lamo tayi a jikin sa, tana jin wani yanayi a jikin ta. Zaunar da ita yayi ya mike ya fita. Kitchen ya shiga ya dauko plate da cups. *MS Indabawa* [1/18, 14:40] Maryam S Indabawa🥰: LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Part *2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 Dedicated to *My lovelly Mum* Don't forget to follow and vote @ MSIndabawa *106-110* *Fateema Kibiya ina miki addi'a Allah ya baki lafiya.* Shi ya zuba musu gasasusun kajin a plate ya dauko lemo ya zuba mata a cikin cup. Mikewa yayi ya dauko ta ya zaunar da ita akan carpet. Ganin baza ta ci ba yasa ya fara bata da kanshi. Ba dan ta so ba ta dinga ci. Duk wannan abin da ake kanta akasa, yake sam taki yadda ta dago bare ya kalli fuskar ta. Suna gamawa ya janyo ta jikin sa. yafara kissing din bakinta nan da nan kwalla tazubo a idonta, Alkebbar jikin ta ya zare mata nan yatsaya kallon surar jikinta yadda tafito acikin kayan data saka, kokarin cire mata riga yafara, yana cirewa yaji jikinta dumi tun alokacin yagane period take nan yaji haushi yakamshi yau ya so ya sami Asma'un sa amma kuma babu dama mensuration ya bata masa shiri, romancing din ta ya fara yi da zafi da zafi, jan na fulaninta ya fara tareda bata zafafan kiss ako wanne lungu najikinta wanda sai da yakwashe fiyeda minti 25 asannan ne yafara kokarin zame skirt din jikinta da yake tagama jigata bata iya yunkurin hanashi ba amma fa ta fashe da wani wahalallen kuka. Haka ya hakura yafara wasa da kirjinta har na tsawon wani lokaci, sai da yadanji dama dama sannan yayi magana cikin narkakkiyar murya Ya ce "yaushe zaki gama?" Banza tayi dashi jin haka yasashi dora hannunsa akan mararta har tsawon minti biyar sannan ya dauke hannunsa. Murmushi kawai ya saki a ransa yace, "Yau ta fara." cigaba da shasshafata Aslam yayi har yasamu nutsuwa yadda ya kamata sannan ya kyaleta yayi hugging dinta ajikinsa sai da ya danyi bacci ahaka sannan yatashi yana kallonta. Asma'u kuwa duk abin da yake tana jin sa sai sanyi da jikin ta yayi. Mikewa yayi ya tafi dakin sa. Wanka yayi yai sallah. Shiryawa yayi ya feshe jikin sa da turaruka, sannan ya fito. Asma'u Kuwa tana can kwance in da ya barta. Tana nan kwance tanata kuka saboda radadin da dukiyar fulaninta suke yi mata. Lallai tin yanxu ma wai, wannan inda abun akai ya zan ji kenan. Jikin ta yai nauyi ma ta kasa tashi. Tana kwance tana zubar da hawaye. Kofar dakin taji ya bude, kai ta dauke tai saurin jan bargo jikin ta. Murmushi yayi ya matso wajen ta. Bargon yayaye, ya kura wa surar jikin ya ido. Asma'u da idon ta ke a rufe, amman tana jin idon sa a kanta. Daukar ta yayi gaba daya yai cikin toilet da ita. Kafa ta fara winsilawa, dan ya sauke ta. Bai saurare ta ba har ya zaunar da ita a kan wata kujera dake cikin toilet. Ruwa ya hada mata ya saka ta a cikin. Wata ajiyar zuciya ta sauke, tai lakwam a cikin ruwan. Shi da kansa ya cuda ta ya gama ya nado ta a towel. Kayan bacci ya saka mata. Ya feshe ta da turarukan ta. Kan gado ya kwantar da ita akan shima ya bi bayan ta. Bargo ya ja mata, ya jata jikin sa ya rumgume ta. Jijjiga ta ya dinga yi har tai bacci. Ya jima yana farin cikin samun Asma'un sa. Yau dai gashi ga Asma'un sa. Yana godiya da Allah da ya bashi ita. A haka shima bacci ya dauke shi. Asubar fari Asma'u ta farka kamar yadda ta saba. Jin ta a jikin Aslam kanekane ya hana ta zame jikin ta. Dan kar ta tada shi. Ta jima tana kallon Aslam tana murmushi. Can taga yai motsi, ido ta tai saurin rufewa, mikewa yai yana addu'ar tashi daga bacci. Kwanciyya ya gyara mata ya shiga toilet ya watsa ruwa yai alwala ya fice. Asma'u na jin fitar sa ta mike ita ma ta fada toilet tai wanka. Tana fitowa ta fada gado. Sai karfe tara ta tashi. Dakin ta ya fara gyarawa, ta fita ta dan sharshare gida ta bade shi da turaren wuta. Kitchen ta shiga ta daura ruwan zafi. A fulas ta zuba, ta fasa kwai ta soya ta wanke plate din. Daki ta koma, tai wanka ta shirya cikin wani purple kala material mai adon yalo. Sosai tayi kyau, simple make up tayi ta rufe kofar dakin ta ta shige bed room tai kwanciyyar ta. Aslam yana dawowa ya tadda dakin a rufe, murmushi yayi yai bangaren sa. Shima kwanciyya yayi. Wajen karfe sha daya Momy ta aiko musu da break fast din su. Aslam aka kira, yaje ya amso. Dakin Asma'u ya kara tabawa ya yaji a rufe. Daki ya koma yai wanka, ya shirya cikin wata Brown kalar shadda. Sosai yai kyau. Fitowa yayi ya kara taba kofar dakin tata. A rufe dai take har lokacin. Knocking dakin yayi, amman shiru. Can ya kara knocking. Muryar ta yaji a hankali ta ce, "Waye?" Murmushi yayi a ransa ya ce, "Waye kuma? Ah lallai Asma'u." "Nine?" Ya fada mata. "Menene?" Ta tambaye shi. "Ki fito ki karya." Ya fada. "Ina zuwa!" Ta bashi amsa. Falo ya koma ya zauna sai da yai wajen awa sannan ta fito. Daining area ta nufa ta hada masa abinda zai bukata. Nata ta diba ta fara ci. Tasowa yayi ya zauna a gefen. Kallon ta yayi ya ce, "Baby na kin ta shi lafiya?" Kai ta dago ta kalle shi da daradaran idanun ta. "Lafiya!" Ta fada a hankali, da ba dan yana kallon ta ba da bai san tayi magana ba. Abincin yaja ya yana ci yana satar kallon ta. Suna gamawa ta koma dakin ta ta saka key. Kallo ta yini tana yi, haka ma da rana Momy ce ta hada masu abincin rana ta aika musu. Shima sai da ya kira ta sannan ta fita suka ci. Sai da sukai sati Momy na aika musu da abinci sannan ta kyale su. Asma'u ita ta cigaba da musu girki. Duk aikin gidan da abinda ya hau kanta da ta tashi da safe take yin su ta gama. Haka nan girki, shima zatayi ta jere masa ya fito ta gaishe shi daga haka bata bashi fuska bare ya kawo mata wata magana. Bangaren sa ma da ya fita aiki zata je ta gyara shi, ta wanke masa under wears nashi ta goge ta turare dakin ta rufo. Duk abinda tasan ya dace tana yin sa sai dai da dare yayi zata rufe kofar dakin ta. Sosai Aslam yake mamakin Asma'u shi dai ya san tabbas Asma'u na son sa amman bai san dalilin yin hakan ba. Wata zuciyar kan fada masa ko dai ta daina son sa ne amman sai ya karya ta. Pretty kuwa taje kano sai da lokacin da ta samu gidan su Asma'u gidan ba kowa sun tafi Abuja. Sai da ta kwana biyu basu dawo ba. Kullum sai taje. A kwanan na ukun ne ta samu Mami a gidam. Iso akai mata Mami ta amshe ta hannu bibiyu, kamar ta santa. Sosai Mami ta burge Pretty dan ita bata xata irin manyan matan na irin haka ba duba da yadda su sukai mu'amala lokacin da suna da arziki suke jin duniyar tasu ce. Sai da Mami ta sa aka kawo mata lemo ta sha sannam ta dube ta ta ce, "Sai dai ban gane ki ba?" Pretty ta ce, "Eh! Wajen Asma'u nazo." Mami ta jinjina kai ta ce, "To gashi bata nan. Tayi aure." Pretty ta ce, "Dan Allah Mama a ina take ina sson ganin ta na nemi gafarar ta." Mami ta kalle yarinyar taga ba alamar mugunta a tare da ita. Mami ta ce, "Tana Abuja acan take aure." Shiru Pretty tayi, can kuma ta ce, "Mama ni ce matar Aslam dan yayar ki. Mama duk abinda ya faru tsakanin Aslam da Asma'u nice sila, ni na yi asirin da Aslam ya daina waiwayar Asma'u duk da bai daina son ta ba. Mama dan Allah ki taimaka ki tayani bawa Asma'u hakuri, nayi nadama dan naga sakayyar Alalh." Kuka sosai take har ta zube akasa. Mami ce ta karasa ta daga ta ta mayar ta zaunar akan kujera. Hawayen fuskar ta ta goge mata ta ce, "Hakika kin raba son da ya dade da kafuwa, son da ba'a taba zaton rabuwar sa ba. Asma'u tayi jinya sosai wace banyi zaton zata warke ba duk a dalilin rashin Aslam. Amman ba komai haka Allah ya kaddara kuma bawa baya wuce kaddarar sa. Allah yayi sai sun rabu kuma sun dawo sun yi auren dai. Zan taya ki rokar Asma'u duk da nasan Asma'u na da saukin kai. Insha Allahu zata yafe miki." Rumgume ta Pretty tayi tana godiya. Da zata tafi har kudi Mami ta bata. Hakan zaman Asma'u da Aslam yaci gaba da kasancewa, ko kad'an bata sakar mishi fuska idan yazo inda take, amma tana masa duk kan abinda zai sa ta. Haka nan girki duk wadan da tasan yana so tana masa, amma da ta jishi zata shige d'akinta, Aslam ma gane hakan yasa wani lokacin baya dawowa gida ko in ya dawo yana bangaren sa, sai dai ya makala nauwara daukar bayani a babban falo kitchen da dakin ta. Wannan yasa ya daina neman takura mata. Dan kullum yana ganin yadda take gudanar da rayuwar ta in baya gidan. Ba karamin burge shi take ba. Bama yaga ta ci ado tana zaune kawai. Ko kuma ta saka kanannun kaya, tai ta juyi ita kadai. Wani lokacin ta kira gida da su Zaianb tai ta waya, haka zata kira Momy ma. Wani lokacin kuma ya ganta tana kuka yakan rasa me yasata kuka. Rayuwa dai kala kala kala take gudanar wa. Abinda yafi burge shi da ita, shine yawan ibadar ta. Yana lura da yadda take dukufa wajen addu'a da nafufuli. Wannan na dada masa son ta da kaunar ta. Kallon rayuwar ta da yake yi, yasa ya daina takura mata da son damun ta. Sai dai yana 'ko'kori wurin kyautata mata sosai da son nuna mata shi masoyinta ne na ha'ki'ka. Yau watanta biyu kenan babu abinda ya canja tsakaninta da Aslam. Tana zaune falon d'akinta ya shigo, bata san ma ya shigo ba tana can duniyar tunani, a fili ta furta, "Allah sarki Dady na ka tafi ka barni cikin wannan duniyar mara dadi. Yanzu banda waji farin ciki." Aslam ya zauna daga nesa da ita ya ce, "Ai ke kika ki barin farin cikin ya sameki." Kamar bazatace komai ba, sai kuma tace, "Waya fada maka, ai farin ciki na nasan ya tafi kenan bazai taba dawo wa ba dan yanzu na rabu da duk masoya na. Kaga kuwa ina farin ciki." Yace "Ni menene naki. Nima masoyin kine na gaskiya wanda ke da burin ganin farin cikin ki a ko da yaushe." Shiru ta mishi ba tace komi ba, Mikewa yayi yayo wajen ta. mikewa tayi da sauri zata fita a dakin. Da sauri ya kamo hannun ta ya zaunar. ya ce, "Haba Husnah ki tunanin zaman mu zaiyi a haka kuwa? Ina mijinki amma bazamu zauna wuri d'aya ba?" Kasa tayi da kanta tana wasa da zoben hanun ta. Wanda shine ya bata. Hannun ta ya kama yana murzawa a hankali. Take tsigar jikin ta ta fara mikewa. Magana ya ke mata cikin wata irin murya mai burkita mai sauraro. "Husnah ki yadda dani wallahi son da nake miki ba abinda ya ragu a cikin sa." Ya fada yana shinsinar wuyan ta. Kamshin ta mai dadi da kwanatr masa da hankali ya shaka take hankalin sa ya fara tashi. Bakin ta yai saurin cafka, yana tsotsa kamar wanda ya samu alawa. Hannun sa ne ya gangara kan dukiyar fulanin ta. Wasa ya dinga yi da ita. Jin yana son wuce guna da iri yasa ta sakar masa wani irin kuka. "Ni dai Yaa Aslam ka kyale ni, wallahi nasan ba sona kake ba. Ka rabu da rayuwa ta dan Allah. Ka koma gun wacce kake so har ka aura. Ni nasan daman Sir ya gama cutata ne da ya bar maka ni. Baza ka taba ganin daraja ta ba." Ta fada yana kuka mai tsuma zuciya. Kallon mamaki ya tsaya yi mata, kasa jurar jin kukanta yayi mai tsuma zuciya, duk ya rikice, ya rasa ya zaiyi, ya fara magana cikin sanyin murya. "waya fad'a miki ina da wadda nakeso bayanke? Wlhy ke kad'ai nakeso Asma'u, ban ta'bason wata d'iya mace a rayuwa ta ba kamar yanda nake sonki, ke ma kin sani ban taba soyayya da wata bayan ke ba. ki bani dama in bayyana miki irin son da nake miki." Da 'karfi tace "baka so na Yaa Aslam, baka so na. Ka koma wajen matar ka da kake so, ni ka kyale ni, nasan dan kaji zan aure ne kazo to kaji dadi da ka raba ni da mai so na." Duk ya rikirkice, ya ce, 'Wallahi banda burin 'bata miki rai 'kanwata, don Allah ki fahimceni, wallahi ina sonki, naayi miki alkawarin faranta miki har iyakar rayuwatah." Hannu biyu ta sanya ta rufe kunnenta tace "Bana sonji Yaa Aslam don Allah ka 'kyale zuciyatah ta huta hakanan, duk abinda zakamin don kasan ina sonka ne...." Kasa karasa maganar tayi ta kifa kanta akan kujera taci gaba da shesshe'kar kuka. Sosai yake jin kukanta a jikinshi, ya rasa yanda zai rarrasheta, hannu ya saka ya d'agota a jikinshi, da sauri ta fara 'ko'korin zamewa, anma tsam ya rumgumeta a 'kirjinshi sosai, har saida tayi 'kara saboda ba ri'kon wasa ya mata ba,. Kuka kawai take dan bata da wani 'karfin da zata kwaci kanta. Aslam kuwa idonshi lumshe, ko lallashinta ya kasayi, duk jikinta ya saki ta fara rage kukan, sun dad'e a haka, kafin ya sassauta mata ri'kon ta zame ta kwanta a hankali ta rufe idonta, shima mi'kewa yayi ya fita ya barta. Sai da ya fita daga d'akin kuma ta fashe da kukan takaici, Aslam yaa riga ya gama da ita tunda ya gane mahaukacin son da take mishi, kuka take sosai a ranta tana addu'ar Allah ya rage mata son sa Ina son ganin comment Follow nd vote @ Msindabawa *MS Indabawa* [1/18, 14:40] Maryam S Indabawa🥰: LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Part *2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* ?? *HAJOW* ?? Dedicated to *My lovelly Mum* *111-115* Da dare da wuri ta mishi girki kafin ya dawo, ta shige d'aki tana gama sallolinta tayi shirin kwanciya, doguwar riga ta saka iyakar gwiwa pink, mai santsi dabin jiki, tayi kyau sosai, mukulli ta saka ta rufe d'akinta ta haye gado tayi addu'a ta kwanta. Aslam kuwa tinda ya fita da yamma yaje gidan Momy. Tambayar da Asma'u tayi ya amsa da tana lafiya. Daga nan Asibiti ya biya, sai da akai magariba ya taho gida. Yana driving ne amma zuciyar sa na can tunanin halin da Asma'u take ciki. Bai son damuwar ta bai son bacin ranta. Dole ya san yadda zai dawo mata da farin cikin ta. Sanda ya isa gidan kamar yanda ya zata, tayi barci ko motsinta bai jiyo ba, d'akinshi ya shiga ya watsa ruwa yayi shirin kwanciya sannan ya fito ya zauna yaci abincin data girka mishi, hankalinshi duk naa wurinta harya gama. A hankali ya murd'a Kofar d'akinta, jinta yayi a rufe, kamar yadda ya zata. komawa dakinshi yayi ya dauko makullanshi yazo ya bude a hankali ya tura kofar ya shiga. K'arasawa yayi inda take, kasa d'auke idonshi yayi a kanta, a fili yake furta, "Alhmdlh, Allah nagode maka da ka mallaka min Asma'u. Ya Allah ka nunamin ranar da Asma'u zata gane irin son da nake mata," tsugunawa yayi saitin fuskarta yana tunanin yanzu da suna zaman lafiya ne zai kwanta da ita ne a kirjinshi yanajin lallausar fatar ta, shi kadai yasan yanayin da yakeji idan yana tare da Asma'u. Abinda ya dade yana fatan ya faru kenan. Hannunshi yakai ya shafi fuskarta, ya d'aura hannunshi saman lebanta, bakin sa ya kai kan nata ya dan sumbace ta. Mikewa yayi ya rufe kofar ya koma dakin sa. Alwala ya kuma yi. Dan Kusan kwanan zaune yayi yana fad'ama Allah damuwarshi. Washe da wuri ta gama masa duk abinda zai bukata sannan ta koma daki. Sai da ta tabbata ya fita sannan ta fito ta gyara gidan Daki ta koma tai wanka tai ado sosai a jikin ta da fuskar ta. Bata san dalili ba yau dai ta tashi da farin ciki da son yin kwalliya. Ta zauna ta karya. Kitchen ta shiga ta fara hada hadar abincin rana. Fried rice tayi wacce ta wadata da hanta, tayi farfesun naman kaji, tayi cislow. Cake ta kwaba tai baking sannan ta yi meat pie. A daining ta jere su tayiwa wajen ado mai kyau. Kitchen ta koma ta hada lemon kwakwa da madara ta saka dabinoi ta sa a firij. Wanka ta kara tai Kwalliya sosai kamar amarya. ta saka wani papper less mai kyau da tsada wanda duk jikin sa stones ne da suka kara masa kyau sai daukar ido yake.. Red and black kala. Sosai tai kwalliya ta feshe jikin ta da turare mai kamshi sosai. Dan kunne da sarka ta saka jajjaye, Babban falo ta koma ta zauna tana kallo. Wajen karfe uku ta jiyo sallamar sa, amsawa tayi ba tare da ta dago ta kalle shi ba. Shi kuwa tin da ya shigo ya zuba mata ido, dan yaga tai masa kyau. Karasawa inda take ya zauna a gefen ta. Dagowa tayi ta zura masa manya manyan idon ta masu dimauta shi, kallon sa ta tsaya yi, sosai yayi kyau. Yana sanye cikin Sky blue din shadda yai kyau da shi. Fatar sa ta dada yin fresh, ya dada haske kyaun sa ya kara fitowa jikin sa ya murje. Ya dawo cikaken balaraben sa Iska ya hura mata, wannan yasa tai saurin dawo wa cikin hayyacin ta. Kai ya daga mata alamar 'Menene?' Kai ta dauke daga kallon sa. Hannun ta ya kamo wanda tai masa ado da jan lalle. Saitin bakin sa yayi da hannun ya sumbata. Zai yi magana kenan yaji ana knocking. "Waye?" Ya tambaya. Mai gadi ne ya ce, "Nine! Bakuwa kayi." "Cene ta shigo." Ya fada yana kallon Asma'u. Mikewa yayi ya ce, bari na shiga na watsa ruwa. Yana shiga tana shigowa ba kowa bace face Pretty. Asma'u da bata san ta ba ta amsa mata sallamar da tayi tana mikewa. Wajen zama ta nuna mata sannan itama ta zauna. Gaisawa sukai, Pretty ta ce, "Baki sanni ba. Ko Aslam yana nan?" Kai Asma'u ta daga ta ce, "Eh amman yanzu ya shiga wanka." Ta mike ta kawo mata lemo da snack. Lemon kadai ta dan sha ta zauna jiran sa. Sai kallon Asma'u take a ranta ta ce, "Ashe haka Asma'un take ahh lallai doke Aslam yaso ta. Duk da yarinya ce amman tana da sura mai kyau. Allah sarki na cutar dake.' Duk wannan maganar a zuciya take yin ta. Sai da tai minti ashirin Asma'u taga Aslam bai shigo ba ta mike ta shiga ciki. Yana gaban mudubi Daure da towel a kugun sa, yana ta kalkale jikin sa, Asma'u ta shiga. Ganin sa a haka yasa tai saurin juya baya. Kallon ta yayi yai murmushi, magana ta fara yi cikin rawar murya, "Kayi bakuwa ana jiran ka." Ta fada, tafiya ta fara yai saurin kamo hannun ta ya juyo da ita. Kin juyowa tayi, shi ya juyo da ita da hannun sa. Ido tai saurin runtsewa. Murmushi yayyi ya jata kan gado. Zaunar da ita yayi ya saka kayansa. Sai da ya gama ya ce, "To matsoraciyya na gama bude idon." A hankali ta fara bude idon ganin ya saka kayan yasa ta bude su. Mikewa tayi ta ce, "Yaya tana jiran ka fa." "Na sani." Hanya tayi zata fita ya ce, "Zo ki gyara ni man." Ya fada yana mika mata turare. Amsa tayi ta fefesa masa. Ta ajiye. tafiya ta fara ya ce, "Oh!" Juyowa tayi, ya ce, "Comb my hair man!" Amsar comb din tayi ta taje masa kai. Tana direwa tayi waje. Bayan ta yabi, suka fita. Hannun ta ya kama, suka jera har zuwa falo. Da yake Pretty ta juya ma hanyar da suke fitowa baya bai gane ita bace Zagayawa yayi ya zauna ba tare da ya kalli bakuwar ta shi ba. Asma'u kuma tayi hanyar sashen sa. Saboda taga yai bakuwa. Dagowa yayi ya ce, "Sann....." Bai karasa fadin abinda zai fada ba yai saurin mikewa. "Me kika zo min a gida?" Ya fada cikin tsawa. Wanda ya janyo hankalin Asma'u. Juyowa tayi ta tsaya kallon sa. Lokaci daya ya canja. Fuskar sa tai jajir, da Hannu ya nuna mata kofa alamar tazo ta fice. Zubewa tayi a kasa tana rokar sa ya tsaya ya saurare ta amman ya kafe akan sai ta fita. Asma'u ce ta koma dakin ta kama hannun sa ta ce, "Haba Yaa Aslam ka tsaya man." Hannun sa ya kwace ya ce, "Bazan tsaya naji ba. ta fice min da gani." Kallon sa Asma'u tayi taga ransa a bace yake sosai. Hannun Pretty ta kama zaunar da ita. Wajen Aslam ta karasa shima ta zaunar da shi. Kansa ta shafa masa har ya samu ya sauke ajiyar zuciya. Kallon sa tayi, ta ce, "Kiyi hakuri duk da bansan me ya faru a tsakanin ku ba amman ka saurare ta" Ta fada tana mikewa. Hannun ta ya kamo, ya zaunar. Kallon sa tayi ya gyada mata kai alamar ta zauna. Zaman tayi, ya ce, "Na baki minti biyu ki fadi abinda ya kawo ki, ki bar min gida na." "Hakuri na zo na baka!" Ta fada cikim sanyin murya. "Indai hakuri ne ki tashi ki tafi bana bukata kara ganin kki a rayuwa ta. Rayuwar da nai dake a baya ma ban san nayi ba." "Nasan da haka Aslam amman ka yafe min, nazo na bawa Asma'u hakuri ne." Kallon ta Asma'u tayi cikin rashin sani ta ce "Ni kuma? Ni da ban sanki ba." "Eh baki san ni ba, amman ni nasan dan har na cutar dake." Kwalar idon ta ta goge ta ce "Dan Allah ki yafe min." Kallon Aslam, Asma'u tayi. Shima kallon ta yayi ya kama hannun ta. Kallon Pretty yayi fuskar sa a hade ya ce, "Malama kiyi mana bayani da zamu gane, da me kika cutar min da kanwata kuma matata." "Aslam tinda na fara son ka kake fada min kana da mata Asma'u ni kuma a duniya na tsani Asma'un nan ganin irin son da kake mata. Duk inda naje ayiwa Asma'u abu sai ace bazai kamata ba dan ba a zaune take ba. Ina shiga damuwa na son ka ga shi kai baka san ma ina yi ba. Wannan yasa naje har nijar na samu bokan da yai min aiki har ka auren ka bar Asma'u." Hannun sa Asma'u ta saki, tana mai zaro ido. Hannun ta ya kara kamawa, Pretty ta ce, "Na maka asiri ka manta da ita da komai nata, sai da naje kano kwanakin baya ake fadan irin halin da Asma'u ta shiga a sanadin rashi ka. Nayi dana sani nayi nadamar raba ku. Dan Allah ku yafe min. Dan naga darasi ga masu bin bokayr yanzu wai ni ke dauke da cutar HIV" Ta fada tana kuka. Asma'u ma kukan take dan ita da wane ido ma zata kalli Yaa Aslam. Aslam ne ya jata jikin sa yana lallashin ta. Amman kuka take kamar me. Ganin ya kasa lallashin ta ya sanya ya kalli pretty ya ce, "To kinji dadi kinzo kin ta dan hankalin mata. Tashi ki bamu waje." "Kayi hakuri banyi haka da zumar bata mata ba. Nayi ne dan na wanke ka. Dan nasan ko yaya ne zata rike ka da abinda kai mata." "Bana son jin komai tashi ki fita." Ya fada yana nuna mata kofa. Hannun sa Asma'u ta saukar ta girgiza masa kai. Kallon Pretty tayi ta ce, "Ba komai na yafe miki haka Allah ya kaddara wa rayuwar mu sai dai kece sila amman Allah ya riga ya tsara. Na yafe miki. Ki nemi yafiyar ubangiji ki." Sosai Pretty tai mamaki haka ma Aslam duk da yasan halin Asma'u ita komai a gun ta mai sauki ne inda zaka nemi yafiyar ta in ka bata mata. Jikinsa ya jata yana rumgume ta sam, Da kyar Pretty, ta ce, "Nagode Asma'u nagode." Aslam ta kalla, ta ce, "Kai ma ka yafe min." Kai kadai ya gyada mata. Mikewa tayi jiki a sanyaye, ta fita. Aslam kuwa tinda ta fita ya kara matse Asma'un sa a jikin sa yyana jin wani tausayin ta. Daman yasan dole rashin sa ya sa ta a wani hali. Shima ya shiga halin mawuyaci Allah ne dai yayi da sauran sa. "Baby nah!" Ya kira sunan ta Kasa amsawa tayi sai, 'Uhmm' da ta fada. Dankwalin kan ta ya zame, yana shafa gashin kanta. Magana ya fara a hankali ya ce, "Baby na yanzu kin yadda ban rabu dake dan son rai na ba. Dan Allah kiyafe min. Wallahi ni mai son ki ne, ina kaunar ki Husnah" Magana Asma'u ta fara a hankali, ta ce, "ka yafemin don Allah ka yafe mu, muyi rayuwarmu cikin farin ciki, wayyo naa shiga uku na cutar da masoyinah, a rashin sani, duk bacin ran bari na da kayi ne, ka koyamin rayuwa dakai, lokaci daya ka guje ni, a lokacin nayi zaton mutuwa zanyi idan har baka tare dani, nasha wahala Yaa Aslam don Allah ka yafe mun ka gafararka mijina." Sambatu kawai take ita kadai, tana kuka, kwantar da kanta ya karayi saman kirjin sa, tana shessheƙar kuka, ji tayi yaa kara matseta a kirjinshi, yaa daura hannu saman kanta. "Baki min komai ba Asma'u duk a rashin sani ne. Na yafe miki Asma'u bazan taba kin yafe miki ba. Ke da abinda kika min da wanda zaki min a gaba duk na yafe miki Asma'u. Ina kaunar ki Asma'u nasan bazan taba iya hada son ki da wata ba. Nai miki alkawarin daga ke ba kari ni naki ne ke kadai. Kamar yadda kike tawa ni kadai. Ina kaunar ki Husnah" Kuka kawai Asma'u take. Dago da fuskar ta yayi yana lashe hawayen fuskar da harshen sa. Sai da ya tabbatar da ta daina kukan sannan ya dago ta sukai daining a cinyar sa ya daura ta ya dinga bata abinci a baki. Sai da ta koshi sannan, ya fara ci yana ci yana santi. Suna gamawa suka koma falo. Rungume juna suka karayi, cikin wani irin yanayi na so da kaunar juna. **** **** Drop ur comment. *MS Indabawa* [1/18, 14:41] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR* *ASMA'U HUSNAH* PART *2* BY *MARYAM S INDABAWA* *MANS* *HAJOW* *HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS* DEDICATED TO *MY LOVELLY MUM* *116-120* ************** Da dare nan Asma'u aka kalkale jiki aka sha gyara akai wanka cikin ruwan turare masu dadi da rikita duk wanda ya shaka. Dan ko da Aslam ya ganta kasa gigicewa yayi. saida sukayi sallah raka'a biyu na godiya ga ubangiji, sun dade Aslam na kwararo musu Addu'o'i, na zaman lafiya da zuri'a dayyiba, sannan suka shafa ya tashi ya barta har lokacin tana addu'ah. Sai data gama ne yace "wannan irin dadewa haka? Me aka rokar mana ne?" Murmushi tayi ta ce, "Ina roka Allah, ya kare mu da sharin mai sharri ya raba mu da duk wani rashin fahimta dazai shiga tsakaninmu, kaine mutum na farko, kuma kai kadai na fara so a zuciyata, ina fatan zamowa matarka har a aljanna. Sannan uwar ya'ya." Yace "Ameen Allah yasa, farin cikinah, idan har Aljanna a tafin kafata take, na rigada na daga miki, ina Sonki sosai Husnah na!" Hannunta yaja yahadata da jikinsa yafara kissing din bakinta, wuyanta da goshinta nan yafara rudata da soyayyarsa tareda janta zuwa gado acikin dabara ya rabata da kayan jikinta nan yafara shakar kamshin dake fita ajikinta, wasannin daya saba yi mata yafara amma na yau yasha bamban dana kullum nan Asma'u tafara fita hayyacinta saboda wahalar yadda yake murza nafulanin ta. Duk kukan da Asma'u take yi bai sashi kyaleta ba dan idon sa ya rufe, sosai yake kokarim shigar ta. Asma'u ta jigata sosai ga azabar datake ji ajikinta, dakyar Aslam yadan kyaleta ta huta in banda hawaye babu abinda take yi, tana dan hutawa Aslam yafara shafarta tareda kokarin maimaita abinda yayi domin ba karamin rudashi Asma'u tayi ba. Nan kuma tafara kokarin hanashi amma takasa dan jikin ta yayi sanyi, sai da yajishi zamzam sannan ya iya hakura amma dakyar ya iya barinta, dakyar tayi masa magana da dasasshiyar muryarta, bani ruwa nasha cikin sauri Aslam yadauko mata babbar robar ruwa yabata tana karba tafara sha bata ajiyeba sai data shanye ruwan ciki tas. Ajiyar zuciya ta sauke. Ta lumshe ido, bacci wahala ya dauke ta. Zuba mata ido Aslam yayi yana kallonta hakika Asma'u ita ce sashe na rayuwarsa, 'Allah sarki yau namiki rashin tausayi Asma'u,' Ya fada acikin zuciyarsa, magana yacigaba da yi, a ransa, "Lallak Asma'u ta daban ce, komai nata daban ne, haka ma ni'imar ta da ban ce, dan yasam ba kowa ke da irin ta matarsa. Yadda yaji ta ya kara dada masa ganin darajar ta da kimar ta. Ta wuce duk inda yake tunani. Amman yasan yai mata ba dai dai ba, tana budurwa yayi sau biyu a lokaci daya. Duk da shi likita ne, To ya zaiyi ya kasa controlling kan sa ne, kallon ta yayi ya ce, "Allah sarki Husnah ki yi hakuri." Juyi tayi, tana mai kara saukar da wata ajiyar zuciyar dan ta sha kuka. Tashi yayi yashiga toilet yayi wanka yai alwala. yafito yasa kayan baccin sa. Sallah yai tayi ta godiya da Allah ya jima yana sallah kafin ya hau kan gadon yaja ta jikin sa. Wani bacci mai dadi wanda ya dade yana mafarkin irin sa ya dauke ta. Sai da Asuba sannan ya tashi yayi sallah amma bai tashi Asma'u ba. yazauna zaman jiran Asma'u ta farka, gefenta ya kalla duk wurin yagama baci kai 'Asma'u yau kinsha wuya' yafada yana shafa gashin dake kwance a hannunta ahankali tabude idanuwanta wadanda sukayi ja kamar jini. Jin jikinta a mace kanta tadauke bata kalli Aslam ba tai Yunkurin saukowa daga kan gadon tayi amma ta kasa. Aslam yai sauri ya karasa gun ta yana fadin "Sannu kin tashi." Hararar sa tayi tafara saukowa ahankali amman sai ta kwala wata irin kara. Toilet ya kai ta ya hada mata ruwa dai dai wanda zata iya shiga. Yana saka ta, ta kwala kara ta kamkame shi tana zubar da hawaye. Duk yadda taso ya cire ta a ruwan ki yayi, sai da ya ji ya huce sannan ya kara hada mata wani ruwan. Nan ma kuka tayi masa. Sai da yai mata ruwa uku duk tana kuka sannan ya barta. Ko a haka ya tabbata yayi aika aika kenan. Wankan tsarki ya taimaka mata tayi yai mata wanka sannan ya fito da ita ya shirya ta. Doguwar riga da hijab ya saka mata. A zaune tayi sallah. Kan gado ya dauke ta ya mayar. Baccine ya daukesu wanda yake cikeda nishadi da annashuwa sai wurin 11 sannan Asma'u farka. Aslam baya dakin kasa sauka tayi daga kan gadon. Idon ta ta runtse, sai ga hawaye. Dakin aka bude, daga kai tayi tana kallon sa. Da sauri ya karasa wajen ta yana ce mata sannu. Daukar ta yayi ya kai ta bandaki. Ruwan wanka ya hada mata. Shi yai mata wanka ya fito ya nado ta cikin towel. Kwantar da ita yayi, ya zare towel din jikin ta, da sauri ta kamkame jikin ta tana masa kuka. Jawo ta jikin sa yayi ya ce, "Husnah ba abinda zan miki, duba ki nake son yi." Kuka ta saka masa. Ba yadda zai yi haka ya kira Dr Yasmeen dan tazo ta duba ta. Kwalliya yai mata ya saka mata kaya falo ya dauke ta ya kai ta. Kirchen ya shiga ya dauko basket. A kasa ya jere musu kayan abincin. Janyo ta jikin ta yayi ya hada mata tea. Doya da kwai ce, sai farfesun kayan ciki da kunun gyada. Kallon sa tayi ta ce, "A ina ka samo abinci?" "Momy na fadawa baki da lafiya ta aiko mana dashi" Da sauri ta dago ta marairaice fuska ta ce, "Kece me yake damuna?" Murmushi yayi ya ce, "Abinda ya faru man.!" "Wayoo Allah na, na shiga uku, Kai Yaa Aslam yanzu haka kacewa Momy" sai ta sa kuka. Lallashin ta ya fara yi, ya dauko ta ya zaunar akan kujera. Wayar sa ce tayi kara, dauka yayi, ya ce, "Ki shigo sai ki shigo kofar dake hannun dama." Yana rufe baki sai ga sallamar ta nan. Amsawa yayi. Asma'u dake jikin sa idon ta arufe ta bude idon ta. Murmushi ta sakarwwa Dr Yasmeen. Zama Dr Yasmeen tayi, suka gaisa da Aslam. Asma'u ta kalla suka gaisa. Aslam ta kalla ta ce, "Me yake damun ta ne?" "Duba ta nake so kiyi, taki bari na na duba ta." Ya fada yana mikewa. Fita yayi ya barsu a dakin. Bedroom suka sshiga. Duba tayi ta girgiza kai. A ranta tan cewa, "Dr Aslam sai kace ba likita ba." Kallon Asma'u tayi ta ce, "ina zuwa?" Ta fita. Aslam na ganinta ya mike ya ce, "Lafiya?" "Eh taji ciwo ne zan dauko abu a gida." "A'ah ga first aid box nan." "No traditional ones za ai amfani dashi." "Ok" Kawai ya ce ta fice. Daki ya shiga ya tadda Asma'u kwance. Sannu yai mata. Murmushi tayi masa. Tausaya ya dinga mata. Dr Yasmeen bata dade ba ta dawo. Sai da ta sanar masa sannan ta dawo dakin. Bandaki ta shiga ta hada mata ruwa sannan ta taimaka mata ya shiga cikin ruwan. Sai da ta gasa ta sosai sannan ta hada mata wani ruwan maganin. Sai da ta kara gasa ajikin ta sannan ta dawo daki tana wata irin tafiya. Zama tayi akan gado, sai da tai mata dinki. Abin tausayi Asma'u dai hawaye take. sallama Dr Yasmeen tai masa, tana fada masa magani da allurar da zai mata. Dakin sa ya shiga, ya dauko First aid box magungunan da zaiyi amfani dasu ya diba ya tafi dakin ta, Dakin ta ya shiga, tana ganinsa ta sunkuyar da kanta, "Sannu Baby na ga magani nakawo miki kinji," Fuska ta bata ya ce "please kiyi hakuru ki sha kinji." karba tayi na dan taso ba tadauki ruwa tasha maganin, ya ce, "To sauranki allura." Ai kuwa nan tace bata san zance ba, maganin ma dan tana jin jiki ne. Kuka ta saka masa, rumgume ta yayi cikin dabara ya zame zanin jikin ta ya tsira mata. kuka ta saka masa bakin ta yai saurin rufe wa da nashi wata iri sumba yai mata. Sai da ya tabbatar tai shiru sannan ya kyale ta. Ranar dai yinin jinya yayi, komai shi yake mata. Abinci kuwa daga na safe har rana da dare Momy ce ta kawo musu. Washe gari da rana suna zaune a falo Asma'u kwance tai dai dai da ita kan Aslam, suka jiyo knocking. Mikewa yayi ya buda kofar Momy ya gani. Nan da nan ya bata hanya, yana amsa jakar ta. Asma'u na jin muryar ta ta mike, a hankali ta karasa wajen ta ta rumgume ta. Zama sukai, Aslam ne ya kawo mata lemo da snack duk dan kar Momy ta gane tafiyar Asma'u. Momy bata dade ba ta tashi ta ce tafiya zatai. Hijab har kasa Asma'u ta saka ta rakata bakin mota. Amman duk da haka sai da Momy ta gane tafiyar ta ba dai dai ba. "Ciwo kika ji a kafa ne?" Momy ta tambaya. "Eh dan bigewa nai dazu." "Ayyah sannu kina kula, zan aiko miki da musu aiki ma." "Kai Momy nagode amman ni zan iya ai ba wani aiki." "Kin tabbata?" Kai ta gyada ta ce, "To duk da haka dai zan kawo miki ko daya ce ta taimak miki da wani abun." "To Momy." "Sai ku ajiye ta a boys quaters ko?" Kai ta daga. Sallama sukai ta tafi tana mai musu addu'ar zaman lafiya. Duk yadda Aslam yake jin bukatar ta hakura yayi dan yasan yai mata aikin rannan sosai Sai da ta watsa ke sanna ya fara nuna mata bukatar sa. Sosai Asma'u ta tsorata amman kuma ba yadda zatai hakkin sa ne. Tin yamma yake rawar jiki da lallabata. Da dare bayan sun ci abinci, da kansa ya dauke ta sukai bangaren sa. Tare sukai wanka duk da Idon Asma'u a rufe yake dan ita wata irin kunyar Yaa Aslam take. Tana mamaki in yana mata wani abu. Takan ce daman haka Yaa Aslam yake. Ya iya soyayya mai tsawa a zuciyar wanda akai wa. A wannan ba karamin wahala Asma'u taji ba, dan ji tayi kamar daren su na farko. Duk jikin ta ciwo, washe gari da asuba tare sukai wanka ya tafi massalaci tai sallah a gida. Bacci suka koma sai sha daya ta tashi ta janye jikinta ahankali tayi kissing din kumatunsa tatashi ta shiga. A hankali take tafiya tana dingusa toilet ta shiga tayi wanka tafito ta shirya ta tsara kwalliyarta cikin wata yar doguwar riga mai hannun shimi ja bata da nauyi ta bi shape din jikinta. Ta feshe jikin ta da turaruka masu kamshi. Kitchen ta tafi ta hada musu break, ta jere su, tadawo dakin inda Aslam yake lokacin ya bude idonsa, hannu ya mika mata cikeda kunya ta karaso tashiga jikinsa. Dan in ta tina yadda suka kasance a jiya wata kunya take ji ita kadai. Kiss yafara bata tako ina yana shakar kamshin jikinta wanda yayi mutukar rudashi, gashin kanta yafara shafawa, ahankali tace "kaje kayi wanka kaji," "uhm uhm nidai kece zaki yimin." yafada cikeda shagwaba dariya Asma'u tayi tasake kamkame shi. Sai da ya gama jagwalgwala ta sannan suka shiga wanka suka cudi junansu sannan suka fito suka shirya, sabuwar kwalliya Asma'u tayi cikin material kore mai kyau wanda yayi mata kyau tayi kwalliya sosai tasha turare shi kuma Aslam kananan kaya yasa thee quarter da bakar riga, hannunta yakama suka fito falo. Dining suka nufa, ya zaunar da ita asaman cinyarshi, abinci ya zuba musu soyayyiyar doya da kwai da farfesun kaji da kunun shinkafa ga wainar da kayan tea, abaki yafara bata har ta koshi. Sannan ta fara bashi a baki wani lokacin idan ta bashi sai yaki sakin hannun nata ko ya dan cijeta da haka tagama bashi. Daukarta yayi yakaita cikin falo ya ajiye ta akan carpet ya kwantar da ita ajikinsa hannunsa yasa acikin rigarta yafara laluben na shanunta ganin rigar jikinta zata rage masa jin dadi yasashi janye zip din rigar hannunsa Asma'u ta rike, ta ce, "Yaa Aslam kabari mana dan Allah " Dariya yayi ya cire rigar ya dora bakinsa akan dukiyar fulaninta yafara wasa dasu da harshensa haka ta kyaleshi har yagama sha'aninsa sannan ya rabuda ita, wunin ranar nan Aslam bai iya koda leka kofar gida ba. Jin sa yake kamar yau ne ranar amarcin su. Don't forget to vote pls *MS Indabawa* [1/18, 14:41] Maryam S Indabawa🥰: LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Part *2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 Dedicated to *My lovelly Mum* *121-125* washe gari tunda wuri ta tashi tafara gyara gidanta, da falo tafara ta gyarashi fes sannan ta gyara part din ta da nashi. Ta shiga kitchen ta gyara, dama daga ita sai yar karamar rigarta mai kamada shimi milk colour shara shara da dan karamin gajeren wandonta iya cinya. Dankali ta dauki ta fara ferayewa, caraf taji hannun mutum akan kirjinta tana jiyowa atsorace taga Aslam ne, tsaye yana yi mata dariya daga shi sai gajeren wando fari da farar best ta maza, ajiyar zuciya ta sauke, duka takai masa ya goce, ta ce, "shine zakazo ka tsorata ni ina aikina?" "Am sorry my Baby love, nima aikin nazo na tayaki to kuma sai naga bamu gaisaba." Murmushi ta dan yi, ta durkusa ta ce, "Ina kwana?" Kallon ta yayyi ya ce, "Ba irin wannan ba." Ya fada yana jan ta jikin sa. juyawa tayi taci gaba da aikinta. "Ni dai ka bari na gama aiki na tukkuna." Hannun sa ya daura akan dukiyar fulanin ta, juyowa tayi ta ce, "Haba Honey love," "Ni ki barni na gaisa da su." Hararar sa tayi ta juyawa, ta ce, "Kai dai Allah yashirye ka dai sam bakajin kunyata," Murmushi Aslam yayi ya ce, "Ina jin kunyarki mana." "A hakan?" Ta fada tana yin aikin ta. Kara jinsa tayi a jikin ta. Ta ce, "To yau baka jin yunea ne?" Murmuahi yayi ya kashe mata ido ya ce, "Indai zan same ki ai ba wata yunwa da zanji." Juyawa tayi ta tana murmushi. Shiru tayi ta kyaleshi saboda tasan idan ta biye masa bazai barta tayi aikin ba. Fita Aslam yayi zuwa harabar gidan har an share an bawa shuka ruwa. Ciki ya koma ya nufi kitchen din ya sameta lokacin tana soya kwai har takusa kammala hada breakfast din duk gidan ya gauraye da kamshi abayanta Aslam ya tsaya ji yake kamar ya rungumeta amma kuma tana aiki, ci gaba da tayata aikin yayi har tagama bayan tagama ta debo kayan ta jera akan dining taja hannunsa ta ce, "zo muje muyi wanka." Jan hannun Aslam, tayi zuwa dakinta inda ta shiga toilet ta hada musu ruwan wanka suka shiga sukayi cikin so da kaunar juna. suna fitowa ta shiryashi cikin Ash din trouser da bakar t-shirt ta fesa masa turaren ita kuma ta shirya cikin wani leshi pink and ash colour ta gyara fuskarta tasha kwalliya tasa jan janbaki tayi jagira tafesa jikinta da turare takafa daurin dan kwali sannan taja. Aslam da ya zuba mata ido ya kasa ko da motsi dan kyaun da tai masa. Juyowa tayi ta sakar masa murmushi. Hannun sa ta kama jikin sa ya ja ta ya rumgumo. fuskar su ya hada da ta shi, light kiss ya manna mata a wuyan ta. Murmushi ta saki ta ce, "Allah love na biye maka baza ka bar mu muci abinci ba." Murmushi yayi ya kama hannun ta suka nufi falo. suka hau kan dining table ta zuzzuba musu abincin tahaye kan cinyarsa tafara cin abincin tana fadin muci, Kai ya makale, ya ce, "A'ah ni ki bani." Murmushi tayi ta fara bashi a baki suna ci yana zuba mata shagwaba. Suna gamawa ta ce, "Yaa Aslam yanzu ka dada ci, karage cin abinci kaga nauyinka yayi yawa gashi sai kiba kakeyi," Murmushi yayi ya ce, "waya fada miki abincine yake sani kiba?" Kallon sa tai da mamaki ta ce, "To meye yake saka?" Daukarta yayi cak ya nufi dakinsa da ita yana fadin muje na nuna miki abinda ke sani kibar, akan gadonsa ya direta ya shige jikinta Yana ya mutsa ta. Ya ce, "kece kike sani yin kiba sugar love," Murmushi tayi ta ce, "Oh ashe ni kake tsotsewa kai kana kiba ni ina ramewa ko," dariya yayi ya kama bakinta ya tsotsa. Ya ce, "Kina son kiba ne?" Kai ta gyada ta ce, "Wai na dan dada kaganni fa." Murmushi yayi ya ce, "Menene baki da shi Hussy, komai na jikin dai dai da shekarun su, basu yi kadan ba. Bama nan." Ya fada yana shafa kirjin ta. "Da nan." Ya shafo kugun ta. Wani yar taji. Murmushi yayi ya ce, "Kuma kinsan me?" Kai ta girgiza, Ya ce, "Sweet din ki ma daban yake, kullun kara dadi kike," Ido ta rufeda tafin hannun ta. dariya yayi ya janye hannun ya ce, "kinsan wani abinda yake bani mamakin?" Kai ta girgiza, ya ce, "A duk lokacin da na kusance ki jin ki nake, kamar a lokacin na fara sanin ki diya mace, kina daya daga cikin matan da suke daban wanda da an gama kusantar ku, wajen ke rufewa ya koma yadda yake," Fuska ta rufe tana murmushi. Hannun ta ya janye, ya ce, "Husnah ke yar baiwa ce, samun kamar ki sai an tona, da na rasa ki da bansan yadda zanyi ba. Ke farin cikin raina. Ina son ki, ina kaunar ki, ki yafen duk abinda nai miki." Ya fada yana shafar dukiyar fulaninta rungume shi tayi tafara kissing dinsa, tasa harshe tafara lasar kowanne sashe na jikinsa shidai Aslam duk tagama ruda shi, kunya ta ajiye agefe tashiga nuna masa soyayya. yafara kokarin cire rigarta, nan ya shiga romancing dinta. Sai da suka shayar da junan su da soyayyar su sannan sukai wanka. Wasu kayan Asma'u ta dauko masa shadda fara kar da farin takalmi da hula tabashi. Da yake ya ce, zai je gun Momy. Da kanta ta shirya shi, ta fesa turare yayi kissing din bakinta yafita, har bakin gate ta rakashi sannan ta koma gida. kitchen ta shiga ta dora girki ta shirya jallop rice with salad tayi farfesun danyen kifi ta zuzzuba acikin flasks tajera akan dining. Ta shiga wanka tafito tayi sallah ta shirya cikin wata riga da skirt na english wears, rigar kalarta pink mai hannun shimi da babban botir guda daya agaban rigar daga kirji sannan ta matse ta sosai ta bayyana surar jikinta skirt din kuma iya gwiwa ne, black kala. ya kama mata hips dinta sun fito. Ribon ta sakawa kanta kawai, ta zubo da gashin gadon bayan ta. tafesa turarruka da humra kala kala tayi kwalliya a fuskarta sannan ta fito falo. Zama tayi ta kunna TV. Can ta mike ta shiga daki. tana fitowa Aslam yana shigowa dagudu taje tafada jikinsa ta rungume shi tafara kissing din bakinsa, fuskarsa, goshinsa da kumatunsa, hannunsa takama zo muje karage kayan nan kazo kaci abinci, kayan jikinsa ta cire masa ta dauko masa, three quater da ramar riga. Shi dai kalon ta kawai yake, sosai tai masa kyau ta kuma ruda shi. Abinci ta zuba musu yana fara ci, yafara yi mata santi yana bata labarin mai Momy. Sun gamawa ya yadauketa zuwa dakinsa agadonsa ya direta yakai hannu yacire botir din dake gaban rigar tata nan yafara wasa da albarkatun kirjinta. Sai da komai ya lafa sanan Aslam yashiga wanka yafito lokacin bacci ya dauke Asma'u. Zama yayi yana kallon ta yana sa mata albarka. Kiran Sallar La'asar da aka kira shi ya sa ya fara shafa kan Asma'u. Ido ta bude, ta kalle shi. Murmushi ya sakar mata ya ce, "Baby na ta shi ki wanka an kira sallah." Mikewa tayi a hankali ta shiga bayi. Kaya ya saka ya fita massalaci. Haka zaman Aslam da Asma'u ya kasance cikin nunawa juna soyayya da kauna da tattalin juna har watanni suka shude kwanaki suka tafi, yau watan su biyar da aure. Tana kiran Mami haka Yaa Buhariin ya shigo Abuja yana zuwa ya ganta. Asibitin ta yana hannun Ya Buhari da Sir Sabir. Suna kula mata dashi. yau tunda wuri Asma'u ta tashi bayan tagama koduwa a hannun Yaa Aslam. Kitchen ta shiga tafara kiciniyar hada musu breakfast yayinda shi kuma Aslam yana can yana gyara musu bedrooms dinsu sai da yagama sannan ya fito. Asma'u tunda tafara fasa kwai taji zuciyarta tafara tashi haka tadaure tafasa tahada ta kada tafara soyawa. Ta soya daya biyu ana uku nan taji zuciyarta tana tashi cikinta yahau juyawa dasauri tadauke kaskon ta nufi dakinta da gudu ta shiga toilet tafara sheka amai kamar zata amayar da kayan cikinta. lokacin da Aslam yashiga ya tarar bata gama ba. Karasawa yayi ya soya. Yana gamawa yabita dakinta a toilet yajiyota tanata aikin sheka amai dasauri yabita cikin toilet din ya riketa har ta gama aman ta kuskure bakinta, a kafadarsa ya daukota ya kaita kan gado ya kwantar da ita, bargo taja ta lulluba saboda sanyi taji tana ji kamar me. Sosai Aslam ya fara yi mata sannu dasauri ya fita yaje ya dauko first aid box dinsa yazo inda take ya zuko allura asirinji ya yaye bargon data rufa tana ganin allurar tafara kuka nan ta hau magiya. Dariya Aslam yafara ya ce, "kinjiki matsoraciya to ranar da zaki haihu yaya zamuyi?" Hawaye tafara taki yarda lallashin duniyar nan yayi taki yarda matseta yayi ajikinsa wata kara ta callara da sauri ya hada bakinsa da nata ya kankameta yajanye rigar jikinta ya soka mata allurar nan tafara fusge fusge amma bai barta ba sai da yayi mata allurar, kwanciya tayi tafara nishi daga nan kuma bacci yayi awon gaba da ita. rigarta Aslam yadaga yafara shafa cikinta da rabon dai Asma'u zaki haifa min yara ya fada yana kissing din cibiyarta. Goilet ya shiga ya gyara sannan ya dawo ya zuba mata ido. Ta jima tana bacci kafin ta tashi tana tashi Aslam ya matso "me zakici maman baby?" Fuska ta yamutsa ta ce, "Maman me?" "Maman Baby na ce." Murmushi tayi ta ce, "Ni din?" Kai ya daga yai murmushi ya ce, "Baby love insha Allahu kin kusa ajiye min Baby. Zan yi farin ciki in har Allah ya azurtani da d'a daga gareki." Kallon sa take da mamaki ta ce, "Sweet love kenan." Ta fada tana mikewa. Toilet ta shiga. Wanka tayi ta fito. Zama tayi tana shafa mai. Gefen ta ya koma ya zauna. Ya ce, "Sannu Baby love." Murmushi tayi ta ce, "Ni fa bana jin komai. Zuciya naji tana tashi kawai." Ta mike ta dauki wani dogon wando tied ta saka, sai yar karamar riga da ta saka. Ta bade jikin ta da kamshi. "Muje kaci abinci." Ta fada tana kama hannun sa. Fita sukai. A falo ta zauna ta hada tea, shima ta hada masa. Dankali ta zuba musu da kwai, ta zuba musu farfesun kifi. Hannu ya sa ya fara ci, tea ta sha kawaai kallon ta yayi ya ce, "Zo nan." Mikewa tayi ta hau kan cinyar sa, dankalin ya dauko ya bata abaki. Amsa tayi ta ci, kwai ya gutsuro ya bata. Tana sawa a baki, taji cikin ta ya hautsi na. Mikewa tayi ya janyo ta jikin sa, kafin tai magana ta fara kelaya amai. Sai da ta wanke shi tas sannan ya lafa mata. Daukar ta yayi ya nufi daki bandaki ya shiga da ita yai mata wanka. Shima yayi sannan ya fito Ya canja mata kaya. Rawar sanyi ta fara kamar dazu, da bargo ya lullube ta. Kallon ta yayi ya ce, "To me kike so kici? Kinga baki ci komai ba." "Wainar shinkafa." Ta fada tana kara shigewa bargo. Mikewa yayi ya zauna yana jijjiga ra. Ya jima dan sai da bacci ya dauke ta sannan ya tashi. Ya mata kiss a goshi ya fita. *Ina son ganin comment da yawa da yawa. Sannan a daure ayi vote* *MS Indabawa* [1/18, 14:42] Maryam S Indabawa🥰: LABARIN RAYUWAR* *ASMA'U HUSNAH* Part *2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 Dedicated to *My lovelly Mum* *126-130* 23/10/2018 TODAY IS ONE OF THE UNFORGETTABLE DAY *INA MAI BAKU HAKURI NA JI NA SHIRU DA KUKAYI MASOYA. KUNSAN JIKI DA JINI. TO JIKIN NE, SAI A HANKALI YANZU MA DAURE WA NAYI NAI TYPING SABODA MUTANE DA SUKE YAWAN NEMA NA AKAN KARASHEN LITTAFIN. AMMAN KUYI HAKURI GA WANNAN NANN NAYI, KUMA INSHA ALLAHI ZANYI KOKARI NAI CONCLUDING BOOK DIN NAN. KO DAN KOWA YA HUTA.* *MY BARRISTER AND FATEEMA TNC DOR UR PRAYER, JIKI ALHAMDULILAH!* *YAN UWA INA BARAR ADDU'AR KU. ALLAH BANI LAFIYA.* *MY LOVELLY BRO BUHARI ABDULKADIR TURAKI. INA TAYAKA MURNAR KAMMALA KARATUN KA. INA ROKAN ALLAH YA BAKA SAKAMAKO MAI KYAU. ALLAH YA BIYA MAKA BUKATUN KA NA ALHERI TARE DA ZURI'A DAIYIBA. ALLAH YA JIKAN MAHAIFI. MAHAIFIYAR KA ALLAH KARA MATA LAFIYA DA NISAN KWANA. INA TAYAKA MURNA SOSAI. WISH U ALL D BEST MY SWTHRT* *MY SWT BRO YAA MUSTY, HAPPY BIRTHDAY. ALLAH KARO SHEKARU MASU YAWA DA ALBARKA. ALLAH BAKA MACE TA GARI DA YA'YA MASU ALBARKA. AMEEN* *MY SON FAUWAZ AND AAYAN HAPPY BIRTHDAY. WISH U MORE YEARS AHEAD.* *KAI YAN OCTOBER YAWA GAREKU, SAURAN SU AUTA TAH. MY YASMEEN ON 31/10/2018 ALLAH NUNA MANA AMEEN YA ALLAH! HBD YASMEEN IN ADVANCE* *DUK YAN OCTOBER KU KIN LISSING SUNAN KU, ZAN HADA MUKU GET TOGETHER DAN AKWAU MUTANE MASU MAHIMMANCI YAN WANNAN SHEKARAR. DUK YAN OCTOBER INA TAYA KU MURNAR ZAGAYOWAR RANAR HAIGUWAR KU. ALLAH ALBARKACI RAYUWAR KU. MUCH LOVE!!* Wani restaurant ya nufa yana zuwa ya samu. siya yayi ya taho gida. Yana shiga ya nufi bedroom inda ya baro ta. Tana cikin bargo har lokacin Amman ta tashi. ajiyewa yayi ya nufi kitchen. Plate ya dauko, da lemon kwali na Mango. Yana zuwa ya zuba mata, dauko ta yayi ya ajiye akan sofar dake dakin.. Lemon ta kalla ta ce, "Na orange nake so " Mikewa yayi da sauri ya nufi kitchen ya dauko ya koma. Sosai taci wainar dan sauran ma a firij ta saka. Tun daga lokacin lafiya ta yiwa Asma'u wuya ga uban amai da takeyi komai taci sai ta amayar. Lemo Kadai take iya sha shima a rana guda daya take yini tana sha. Momy kam ba karamin tausayawa Asma'u take ba dan ta rame. Da ta ce Asma'u ta koma gidan ta har kuka Aslam yai mata dole ta barta. Amman kullum tana hanya zuwa duba ta. Da Aslam yai wa Momy korafi akan aman da take yi. Momy cewa, tayi, "Ai wannan Aman na lokaci ne, lokaci daya zata daina sai a hankali." Mami ma da taji Asma'u na da ciki tayi murna. Haka Zainab da takanas tazo duba ta, tana ganin Dadyn ta ta farai masa wasa. Sosai tai murna da zuwan Zainab komai ta dauko Zainab da Dadyn ta, ganin su ma sai yasa ta warke. Dadyn ta kuwa kullim yana gun ta yaro ya dada wayo dan har an yaye shi ma. Kwana biyu sukai ta koma. Asma'u na cewa ta bar mata Dady. Zainab ta ce, "Kiji da na cikin ki ma." A lokacin ita kuma Nusaiba ta haifi dan ta Namiji aka saka masa sunan Dadyn Sabir Marzuk suke kuran sa da Fauwaz. Itama Zainab tana da yaron ciki a lokacin. Maimuna ma ta haifi yar ta mace aka saka mata ssuna Asma'u. Suke kiran ta little Husnah. Asma'u ce kwance acikin kujera a falo shi kuma Aslam yana kitchen yana soya mata wainar fulawa, falon ya kawo mata ta tashi tafara ci sai data cinye tafara sheka amai shi kanshi Aslam sai data wankeshi da amai, rigar jikinta ya cire mata yafara gogge mata jikinta. Ido ya zuba mata, kirjin ta ya kara cika, haka nan hip din ta sun bude. daukarta yayi yakaita toilet yayi mata wanka shima yayi yadaukota yakawota daki. Magani ya bata ta sha sai bacci. Yana tausayawa Asma'u dan tana sha wahala sosai. Ido ya zuba mata, ya ga ta rame sosai. A ransa ya ce, "Wannan Babyn yana wahalar min da Honey bae ta." Jikin ta ya shiga ya kwanta. Baccin ne shima ya dauke shi. Sai da cikin Asma'u ya girma sannan ta samu sauki. Tin daga lokacin kuma sai kwadayi ya bude. Komai tasa a kawo mata. Momy kuwa yau ita ce kai mata kaza gobe kaza duk abinda tasan zata ji dadin sa. ******** Cikin Husnah ya girma haihuwa ko yau ko gobe. Komai Aslam ne, ke yimata hatta wanka da wanki shine yake yi mata. Yau tin rana take jin ciwon ciki amman bata fadawa Aslam ba. Har dare suka kwanta. cikin dare ta tashi da ciwo. Nan Aslam ya tashi ya duba yaga haihuwa ce. Kasacewa tin da cikin ta ya shiga wata tara ya debo kayan da zasu bukata ko da irin haka ta faru haihuwar dare kenan. cikin kankanin lokaci ta haifi jariranta tagwaye guda biyu duk maza nanfa Aslam yafara murna. Shi ya gyara ta, yai mata wanka ya shirya yaran sa. Gari yana wayewa ya fara shelar fadin haihuwar Asma'u Ai kuwa yan uwa da abokan arziki suka yita xuwa ganin jariran. Da Momy ta zo, take cewa Asma'u gida zata tafi ayau sai tayi 40 zata dawo, nan kuma Aslam yace bai san zancen ba babu inda Asma'u zataje Fada Momy ta rufe shi dashi ta shiga hadawa Asma'u kayanta. Tana mitar yarinya aure shekara daya da wata hudu bata je gida ba sannan ta haihu ma baza ka bar ta taje ta huta ba. Asma'u kanta bata son tafiya tabarshi amma, tana son taje gida a kula da ita. Duk da tasan shima zai kula da ita amman kuma zata kara hutu bare ma yara biyu ai sai da taimako. Momy da kanta ta kai Asma'u har Kano nan Mami ta shiga murnar ganinta. Aslam kuwa tunda ta tafi bai kirata ba dan fushi yake wai meyasa zata tafi bada izininsa ba, ko kanon ma yaki zuwa. Sai dai duk abinda ake bukata ya turawa Momy shi dan Momy ta ce, sai anyi suna zata koma. Ana gobe suna sai ga Aslam, da kaya niki niki. Dan set din alkwati ya ciko musu kowa da kayan sa. tinda yaje ya dauki yaran ya kasa ajiye su. Sosai yake jin kaunar yaran a cikin ransa yana mai godewa Allah da ya azurta shi da yara har biyu duk maza. Anan yai musu huduba da Suleiman, Sunan Dadyn Asma'u sai Muhammad sunan Dadyn sa. Ranar suna anyi shagali sosai inda yara suka ci suna Suleiman da Muhammad. Anyi shagali dan duk kawayen su Asma'u sun zo na makaranta. Maryam ma taje a lokacin tana da yaron ciki. Anyi bikin ta da Naufal lokacin Asma'u ba lafiya wannan ya hana Asma'u zuwa sai sako da ta aika mata. Sosai Asma'u tai murna da zuwan ta. Haka Nusaiba ta zo ita ma da kayan barka da Danta Fauwaz ya girma dan watan sa hudu. Ana gama shagalin suna Aslam da Momy suka fara shirin tafiya. Aslam kuwa ya san. Zai yi missing din Asma'u ace sai tayi arba'in. Tana daki a kwance taci ado sai fitar da kamshin take, su yan biyu suna wajen Momy. Dakin taji an turo, daga kai tayi ta kalle shi. Murmushi ta aika masa ya karaso cikin dakin. kusa da ita ya zauna ya tsura mata ido tana sanye da jar atamfa mai ratsin baki ajiki tayi dan kwaliyya jikin ta ya murje, kirjinta ya cika sosai. Janyo ta yayi jikin sa, can kuma ya daga ta, ahankali yadaga rigarta ya kwantar da kansa acikinta, Wasa ta fara da gashin kansa. Ya ce, "Husnah kice zaki bini dan Allah." Murmushi tayi a ranta ta ce, "Da yake gani uwar marasa kunya ba." Mikewa yayi ya ce, "Baki ce komai ba." Ta ce, "To me zance? In nace zan bika ai nayi rashin kubya ko?" Kai ya girgiza ya ce, "ba wani rashin kunya." "Hmm!" ta fada tana wasa da yatsun hannun sa. "Wallahi zan shiga wani hali in bakya tare da ni. Ki taimaka kizo mu tafi kinji love." Dariya ta dan yi ganin da gaske dai Yaa Aslam yake. "Au dariya kike?" baki ta danne da hannu ta girgiza kai. "Shikenan Allah aure zan kara." nan take taji gaban ta ya fadi. Dagowa tayi ta kalle shi sai kuma ta dauke idon ta. Mikewa yayi ya fice ya barta cikin fargaba da tsoro. Washe gari da safe sai a falo ma tajiyo shi, mutumin da adakin ta suke karyawa. Yana zaune yaran sa akan cinyar sa yana ta daukar su hoto. Zama tayi a gefen sa ta dan rage murya ta ce, "Ina kwana?" Bai kalle ta ba duk da kamshin da take yana fizgar sa, amman ya maze ya cigaba da abinda yake. Ayman ta dauka, wato usaini mai sunan Dadyn Aslam. Sannan ta dauki, Aayan mai suna Dadyn ta. Tana amsar su ya mike yayi dakin sa. Shayar dasu tayi sannan ta mike ta shiga dakin Mami. Suna zaune Mami da Momy. Sai da ta gaisar da su sannan ta mika musu Baby. Momy ce ta mike ta ce, "Bari na kira Aslam yazo mu tafi." Ta fice can sai gasu sun shigo, Aslam ya canja shiga zuwa wata Ash kalar shadda. Yayi kyau, kamar ka dauke shi. Sai tashin kamshi yake. Akwatin ya dauka ya sauka sannan ya dawo Mami ce ta mike tabi bayan sa. Momy ta kalli Asma'u ta ce, "Asma'u zamu tafi munyi magana da Mamin ki mun yanke zaki wata uku saboda yaran su kara kwari kin haihuwar fari ce kina bukatar kulawa. Naso ki zauna a guna amman naga tinda kikai aure baki zo kinga Mamin ki ba. Amman wata haihuwar ni zan kula dake. Da kai na zan zo na dauke ki in lokacin yayi. Duk abinda kike bukata kina sanar dani " Ta karasa maganar tana shafa kanta. Tace, "Ki zauna mun tafi Allah kara lafiya." Momy ta fita. Asma'u kuwa hawaye taji yana zubo mata Ta ce, "shikenan sai yai auren da yace zai yi." Mikewa tayi takarasa window tana kallon su, suna shiga mota. Aranta tace, "Lallai Yaa Aslam ko ya min sallama." Waya ta dauka ta tura masa da text din Allah ya kaisu lafiya. Ta koma ta kwanta akan gadon Mamin ta. *BANYI ALKAWARIN ZAKU SAMU UPDATE NAN KUSA BA AMMAN YADDA NAJI JIKI NA ZAN KOKARTA DAN IN GAMA NIMA NA HUTU.* NAGODE DA KULAWAR KU *MS Indabawa* [1/18, 14:44] Maryam S Indabawa🥰: LABARIN RAYUWAR* *Asma'u Husnah* Part *2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 Dedicated to *My lovelly Mum* *131-135* Alhamdulilah jiki Alhamdulilah wallahi sai godiyar ubangiji. Nagode da addu'ar ku fans musammam yan group din Zama na Amana 2 da khaleesar haidar. Nagode Allah ya bar zumumci Ameen  Wannan shafin nakune na duk mai suma Hauwa'u, Jidda, Yasmeen kuyi yadda kuke so dashi duk dan sbd da jin dadin Autar mu Hauwa yasmeen Tin daga ranar Aslam bai kara kiran ta ba dan yai fushi sosai duk da yana son yaji ta sai dauriya da yake sai dai ko ya bugi cikin Momy ko in suna waya yana musu labe. Sosai Asma'u ta damu, amman kuma tana cikin jin dadi da kula da hutu. Mami bata barin ta da kadaicin da zata zzauna tinani. Ba abinda take a gida daga wanka sai bacci. Ko yaran sai zasu sha mama ake kawo mata su. Gyara kuwa da wanka sosai Mami ke mata dan jkin ta har ya saba gashi Mami ta ce wata ukun nan sai an mata wanka dan haihuwar fari ce kuma ya'ya biyu dole a gyara ta in ba haka ba faba zata ji jiki. Sai anan ta gane manufar da akace sun ka je gida. Dan ta godewa Momy da tace lallai lallai sai ta zo kano, Tana shan gyara banda cima da Mami ta canja mata. Sosai ake kula da ita. Kuma akai akai Zainab da Nusaiba da Maimuna suna zuwa duba ta. Sai dai tausayin Aslam da take ji dan ta san waye Aslma bama akan bukatar sa. Baya iya jure rashin ta gashi wai sai tai wata uku abin da kamar mamaki tasan yanzu yana can yanda takura. Abinda yafi tsaya mata ma arai kar yaje yai auren da yace zai yi da ya zatai zatai sharing din sa da wata in ta a har kuka tkeyi. Aslam kuwa yana can yana ta lisafin arba'in. Ranar da sukai Arba'in a ranar ya dauki waya ya kira ta dan a lokacin ya huce. Tana dagawa, ya farai mata sururai na irin murna da yake zata dawo. Shiru tayi a ranta ta ce, "Bayan ance sai nayi wata uku " "Ba kyaji nane?" Y fada. "Uhmm ina ji." "Amman kikai shiru. Kiyi hakuri ban daina kiran ki dan komai ba sai dan gudun kar na shiga wani hali in na kira ki. Wallahi da kyar nake iya bacci ina missing naki Husnah." Ajiyar zuciya ta sauke. Ta ce, "Sai hakuri, tinda kaga su Momy sunce sai nayi wata uku zan dawo. Ka kara hakuri nima ina kewar ka." Ido Aslam ya zaro, ya ce, "Wata uku." Kai ta gyada. Wayar ya kashe a ransa ya ce, "Wallahi bazan iya ba matata zan dauko." Baiwa Momy maganar ba ma ya fara shirin tafiya kano. Yau ya dira a Kano. Gida yayi kai tsaye. Mami bata nan taje unguwa gida ya rage daga Asma'u dake dakin ta tana bacci ita da yaran ta. sai mai kula da yaran a kasa. Yana zuwa suka gaisa ya tambayi Mami aka ce bata nan. Sama ya hau dakin Asma'u ya shiga. Tana kwance, tana bacci tana sanye farin less dinkin riga da siket Ba kwalliya a fuskar ta amman tayi kyau dakin da ita sai tashin kamshi take. Zama yayi a gefen ta ya zuba mata ido. Kan sa ya daura akan kirjin ta. Cikin bacci taji kamar kamshin turaren Aslam. Ido ta bude ta ci karo da fuskar sa. Ido ta mutsuka ta mike zaune. Zama ya gyara, Aslam ne, dai, yasha shadda brown colour da hula sai zuba kamshi yake. hannunsa takama ta ce, "yaushe kazo?" Ya ce, "Nazo kinata bacci." Murmushi tayi. Jikin ta ya shige, ya rumgume ta. Motsin su Aayan da Ayma ne ya sa ya juya. Suna cikin gadon su, mikewa yayi ya dauki, Aayan ya ajiye a cinyar ta sannan ya dauko Ayman. Mama take bawa Aayan tana gamawa ta mika masa shi ta amshi Ayman shima tana bashi. Yaran ya zubawa ido yana kalla tamkar yayi kaki ya ajiye saboda tsananin kamarsa dasu yaran an saka musu kaya iri daya pink din riga da blue wando sai farar rigar sanyi a sama. Yan yatsun hannun Aslam ta murza, kallon ta yayi ya kasa dauke ido. Ta ce, "yadai?" Tafada tana kallonsa. Murmushi yayi yai wa Aaayan addu'a sannan ya ajiyr shi. Ayman ya amsa shima yai masa addu'a ya kwantar a gefen dan uwan sa. Kallon ta ya tsaya ta ce, "Ya dai?" Bai bata amsa ba sai kan sa da ya sunkuyar a cibyar ta. ya tura kanshi cikin rigarta ya fara lasar cibiyarta. Murmushi tayi tashafo sumar gashin kansa tace "Honey Love ya hanya?" Shiru bai bata amsa ba domin duk ta gama tafiya da hankalinsa, ita kanta yatafi da imaninta saboda kamshin turarensa kadai yakashe mata jiki. Dagowa yayi ya ce, "Nazo na tafi da kune." Ido ta zaro ta ce, "Haba dai." "Oh bakya son ki koma?" Kai ta girgiza. kiss yabata akan lips dinta "yawwa baby gobe zamu tafi to." Murmushi tayi ta ce, "Allah kaimu." Sati yayi sannan ya koma da kewar su. Haka ending month ma ya koma a lokacin watan su biyu da sati biyu. Tunda Aslam ya tafi ya fara shirin karbar Asma'u gaba daya gidan ya sake mata komai sabo tun daga kan furnitures har fentin gidan komai yadawo sabo kamar gidan amarya. itama Asma'u acan sosai Mami ke gyara ta. Taje gidan Uncle Habu da Kanwar Dady Momy Binta da Uncle iliyasu. duk sunji dadi sukai mata alheri. Sannan taje grin su Mami wajen yan uwan su Mami. Kwananta bakwai ta dawo. Sannan ta zaga kawayen ta. Suma da suke yawan kai mata ziyara. Har gidan Maman zainab da Mamayn Sir Sabir taje. A daren ranar kuma sai ga Sir Sabir da Nusaiba da Baby Fauwaz. Sun gaisa ya daumi yara yana tai musu addu'a. Da zasu tafi ya ajiye musu dubu dari ya ce a sai wa yara riguna. Tai masa godiya har wajen kota ta rakasu sannan suka tafi. Ranar Alhamis sai ga Momy nan. Nan tasan lokacin lafiyar ta ne yaxo. Zainab ta fadawa Zainab tazo ta dauke ta kai ta aka gyara ta. Akai mata lalle, da gyaran gashi tafito ral kamar amarya. Ranar a gidan Zainab ta kwqna. Zanab ce dafa wannan takai mata haka nan Yaa Huhari duk ya debe yaran ranar yaran gun su suka kwana. Dan Yaa Buhari akwai son Yara. Washe gari ta daqo gida Zainab ce duk ta hada musu kayan su. Momy ma da taga yaran taga sun yi saurin girma ta kalli Mami ta ce, "Amina me kike bawa yaran nan naga duk sun kara girma da kyau bama 'ya ta." Murmushi Mami tayi ta ce, "Nima ina mamaiin girman yaran nan sai kace ba yan biyu ba." Momy ta ce, "Daga nonon Maman ta sune." Ranar kusan kwana sukai ana hira da su Mami dan Asma'u sai bar musu yaran tayi ta tafi ta kwanta. In da washe suka dau hanya. Suna zuwa Momy gidan ta ta kai ta. Gidan da ta ga ya canja, kamar sabon gida. Tayi mamakin irin aikin da akai a gidan dan za ta ce har gidan yafi lokacin da ta tate kyau da tsari duk yadda wancan tsarin yayi kyau. Tare da Mama mai taya ta raino suka tafi. Lokacin da suka je Aslam baya nan. Dan haka ta hau gyaran gidan Ta debe su Yaman ta kai ma Mama dan ta rike mata su. duk da ba wani datti yayi ba komai tsab yake. Haka ta kara gyara shi ta turare shi da turaren wuta mai dadi da kamshi. Tini gidan ya kara kau da fitar da iska mai dadi. kitchen ta dora Coconut rice sai miyar da tayi ta zuba kji. tayi da farfesun hanta, Bayan ta gama ta diba ta kaiwa Mama. ta dauko yaran tai musu wanka ta shirya su ta sa sukai bacci. itama tai wanka ta shirga cikin body hug ja da bakin wando takama gashin kanta da jan ribom, sai da ta turare gidan da kanta da daddadan kamshi tukunna tazauna a falo tana jiran zuwan Aslam. Har akai isha'i bai shigo ba. Tana kwance tana kallo yana shiga ya hangota zaune cikin kujera das da ita tamkar budurwa. Tsayawa yayi yana kallonta tana juyowa suka hada ido ya tsuke cikin Ash suit, tasowa tayi tazo ta shiga jikinsa tana magana a hankali "sannu da zuwa Honey love," kasa magana yayi ya cafki bakinta yafara tsotsa tuni itama tafara mayar masa da martani, ganin tsaiwar zata gagaresu yasata kama hannunsa zuwa bedroom dinsa suna shiga yajata kan bed, ya kwantar da ita ya fara sinsinar ta rike shi tayi tace, "ka zo kaci abinci," "bazan iya ba." yafada acikin kunnenta "To tsaya na taimaka maka da cire kayan." A hankali ta fara cire masa. Jan ta yayi ka gado, kayanta yafara cirewa dasauri dasauri nan yashiga nuna mata zallar so, sai dai ita Asma'u ji tayi kamar ranar farkonsu dan dakyar ya iya shiga ga wani radadi da takeji, shi kam Aslam washar dashi dan ji yayi Husnahn Sa tadawo sabuwa fil. Soyayyar da ya nuna mata ta tsaya mata a rai dan baza ta taba mantawa da wannan irin soyayyar ba. Sosai ya nuna mata irinnyadda yai kewar ta da yadda ya ke jin ta a ran sa. Bayan komai ya gama wanzuwa ne Aslam ya jata jikin sa yana zuba mata mata albarka sun jima a haka yana shafa gashin kanta. Sannan ya ji tana saukar da numfashin ta a hankali Dubawa yayi yaga har tayi bacci. tashi yayi yashiga wanka yana cikeda annashuwa yana fitowa yanufi dakinta acan yaga twins dinsa sunata bacci Dakin da take ya koma. Har lokacin tana bacci. Kanta ya shafa a hankali yana hura mata iska a cikin kunnen ta. Ido ta bude, ta tashi daga baccin, kallon Aslam tayi da idonta jajur duk jikinta ciwo yake yi mata gashi ji take ko tafiya bazata iya yi ba. Fuska ta shagwabe, ta ce, "zanyi wanka." tafada tana turo baki. Murmushi yayi ya mike ya shiga bandaki ya hada mata ruwa. *Dont forget to vote* *MS Indabawa* [1/18, 14:45] Maryam S Indabawa🥰: *Asma'u Husnah* Part *2* Na *Maryam S Indabawa* *Mans* 🌐 *HAJOW* 🌐 Dedicated to *My lovelly Mum* *136-140* *END* HAPPY BIRTHDAY AUTAH INA MIKI ADDU'A ALLAH YYA RAYA KI YA BAKI.MIJI NA GARI YA BAKI.YA'YA MASU ALHARKA YA BAIKI ILIMI MAI AMFANI ALLAH YASA KI GAMA LAFIYA AMEEN. YAU RANAR KI CE AUTR MU KIYI ABINDA KIKE SO KINA DA MU YASMEEN U RE A LOVELLY SIS AND ALSO MY BESTY WHO I SHARE MY PROBLEM WITH HER SUK DA SHE IS YOUNG VUT SS SO SWT TO ME AND TO EVERYBODY WHOSE KNOW HER WISH U MORE BENEFIT YEARS AHEAD MY AMINIYYA (OH ASHE FA TA CE NICE AMINIYYA ITA KUMA VESTIE) LOVE U AUTAH HAUWA'U USAMAN (YASMEEN) Daki ya koma ya dauke ta ya kaita bandaki. Shi yai mata wanka dakyar ta iya taka kafarta tadawo daki tana dawowa tawuce dakinta ta kintsa tasa wata doguwar riga iya kar ta cinya. batayi wata kwalliya ba tadawo dakinsa. Yana zaune, ta ce, "zo muje kaci abinci danni yunwa nakeji sosai," Tashi yayi daga shi sai gajeren wando sukaje falo dakyar take tafiya suna zuwa ya kwaso musu abincin ya kawo kan carpet ya ajiye yafara zuzzuba musu nan tafara ci. kallonta Aslam yayi, ya ce, "sannu baby, Allah miki albarka." Batayi masa magana ba har sai data koshi. Kallon ta ya sake ya ce, "Sannu!" Hararar sa tayi ta ce, "Eh ai ka min sannun, wallahi Yaa Aslam baka bina ahankali koda yaushe da karfi kake yi min," Ta fada tana turo baki. Dan tsotsar bakin yayi, sannan ya ce, "kiyi hakuri ba laifaina bane," Mikewa tayi ta shiga dakin ta. Duba su Aayan tayi taga suna bacci. Falo ta dawo ta hau kan kujera tamike kafa. Biyo ta yayi yana mata tausa. Ido ta lumshe, ya ce, "Ba tin yau ba na fada miki a irin jinsin matan da kike. Ku kalilan ne, wannan yasa kike jin jiki a duk lokacin da nai kwana biyu ban kusance ki. bare yanxu wata uku fa. Ai dole. Ni kam naji dadi na. Na samu yar baiwa, wace ko da yaushe take a budurwar sabuwa." Ido ta bude tana kai masa duka. Hannun ta ya kama, ya fara kissing na ta. Nan da nan jikin ta yai sanyi. *************** Tsakanin Aslam da Asma'u zamane suke yinsa na kaunar juna da soyayya, yaransu sun girma sunyi wayo yanzu watansu 9 amma idan ka gansu zaka zaci sun shekara daya dan suna gudun ko ina. Sosai suke Samu kulawa daga wajen iyayen su da Kakkanin su. Dan in suka ga Momy ko Mami har wani shagwaba suke musu dan sun san abinda suke so shi za ai musu. Zaman lafiya mai hade da soyayya da kaunar juna shi yake wanzuwa tsakanin Aslam da Asma'u. Su Yan biyu na da shekara hudu Asma'u ta sake samun ciki. A lokacin har an saka su a makaranta. Yara kyawawa da su abin sha'awa. Wannan cikin alhamdulilah ba wani laulayi sai kwadayi. Daga ta ce, kaza take so sai ta ce kaza. Aslam kuwa yau shine dafa wancan soya wancan dan in ita tayi bata iya ciki. Duk da haka tana kokari wajen kula da gidan da mai gidan ta. Wannan karan ma yan biyu ta haifa duk mata. Akasa wa hassana Fatima, suke kiran ta Nabihah sai usaina Amina ake kiran ta da Nabinah. ********--------********* *BAYAN SHEKARA 12* Sanye take cikin wani tamfatsatsen leshi mai kyau baki da ja. sai kamshi take zubawa, falo ta fito babu kowa, ta tagar baya ta leka. Hangon su tayi, Aslam na zaune rike da jarida. yana sanye da three quarter da yar karamar rigar shan iska. Sai Aayan da Ayman suna buga ball. Sun saka kayan ball a jikin su. Da ka kalle su zaka ga kamar su daya da Aslam ba abinda suka baro shi. Kamar ya'yan labara bawa ko da yake baban su jinin larabawar ne. Gefe kuma Nabibah da Nabinah ne, sai Autar su, Husnah wacce shekarar ta hudu, suke kiran ta da Nawal. Sun zaune suna duba littafi. Suna sanye da farin dogon wando da pink riga. Kansu an musu parking da pink ribon. Kafar su ma pink cover shoe ne. Can Aslam ya mike yai Cikin gida. yana shigowa ya hangota tsaye tana kallon yaransu ta window, bayanta yaje ya rungumeta akoda yaushe son Asma'u yake ji yana shigarsa sosai gata dai haihuwarta uku yaranta biyar amma har yau bata gundurarsa. Juyowa tayi ta rumgume shi ita ma. kissing nasa ta fara ko ta ina. Ganin tsaiwar baza ta dauke su ba yasa ya dauketa cak a kafadarsa yayi cikin dakinsa da ita. A Kan gado Ya kwantar da ita yafara yi mata wasanni masu rikitarwa. Sosai suka shayar da juna su zumar soyayya tsadadda sannan sukayi wanka suka fito, kwalliya suka sake tasaka yellowar atamfa shi kuma yasa blue kalar shadda. Mayafi ya dauko mata suka fice daga gidan. Hanyar cikin gari taga sun nufa. Kallon sa tayi tace, "sai ina?" Murmushi yayi ya ce "Rufe idon ki!" Idon ta ta rufe. Parking yayi ya fito ya bude mata site din da take. Hannun ta ya kama ya ja ta. Dai da suka tsaya samnam ya ce, "Open ur eyr my queen." Ido ta bude, wani katon asibiti ta gani a gaban ta. Kai ta daga, ta ga an rubuta *ASMAAAF CLINIC* Ido ta bude ta ce, "Means?" Murmushi yayi ya ce, " *ASMAAAF* Means, Asma'u, Suleiman, Muhammad Aslam, Amina, Asma'u, Fatima." Rumgume shi tayi, ta ce, "Yayi kyau!" Murmushi yayi ya ce, "Naki ne!" Kallon sa tayi da mamaki ya ce, "Kin wuce haka a guna Asma'u. Kece farin ciki na rayuwa ta cikar buri na. Banda abinda zan saka miki da shi sai dai ina miki addu'a Allah ya biya miki bukatun ki na alheri Allah ya hada mu a gidan Aljanna dani dake da yan uwan mu musulmai baki daya." Rumgume shi ta yi sai kuma kuka, ba wanda ta tino sai da Dady da ya ke ce mata Ko baya raye ya bar mata farin ciki. Farin cikin ta kuma sune Aslam da Yaa Buhari da Mamin ta. Lallai yau ta dada yadda Yaa Aslam da Yaa Buhari da Mamin ta sune farin cikin ta. Tana kara godiya ga Allah da ya mallaka mata Uwa kamar Mami. Ya bata Yaya kamar Yaa Buhari mai burin ganin farin cikin ta. da kyautata mata kullum burin sa ganin ta bata da damuwa tana cikin farin ciki da walwala Sannan ya bata Miji Yaya kamar Yaa Aslam wanda samun kamar sa sai an tona. Kullim.cikin kaunar ta da nuna kata kyautar ta yake. Bai da buri sai.na yaga ya kyautata mata. To.ita kuwa mai zatayi in ba addu'a gare au ba. Tare da Dadyn ta da Mami da Yayun nata. Daga nan gida suka yi. Suna komawa ta shiga kitchen. Ita ce girka wancan dafa wancan. Dan karamar walima ta hada musu a gidan aka ci aka sha akai hoto. Sannan ssuka zauna kamar yadda sukai akai hira anan kuma. A zauna ai karatun al kur'ani wanda duk dare kan a kwanta da asuba in an tashi sai anyi izifi daya gaba dayan su. daga nan za ai ta bada labari bama Husnah da kullum sai ta basu labarin Dadyn ta. Wanda suke ji daman yanan ja suma ya nuna musu tashi kalar soyayyar. Duk akn su sun san Dady kuma kullum akai sallah sai an masa addu'a Allah jikan sa.Nawal kuwa da ba wayo takan ce "Ummu ki ka' ni gun Dadyn ki." Sai dai Asma'u tai murmushi ta ce, "Zamu je gun sa amman sai munyi aiki na gari a rayuwar mu. Dan Dady mutum kirki ne." Abibda Dady ya roka ta cika masa dan yaran sun tashi da son sa da masa addu'a in kaji ana labarin Dadyn Asma'u sai kazata yana da rai wani abun. Sun jima sannan kowa ya je ya kwanta. Sai da tai wanka sannan ta fito daure da towel Aslam ne yashigo dakin. Tsayawa yai abakin kofa ya harde hannu a kirji. Kallon ta yake yadda kugun ta yake juyawa. murmushi tayi ya karasa wajen ta. Turare take shafawa ya karasa, kugunta ya rike yace "shekaru goma sha uku kenan amman har yanzu kina nan a yadda kike, ko ma nace kinfi da dadi." Ya karasa maganr yana rada mata wani abu. Juyowa tayi ta daura hannun ta asaman kafadar sa, ta ce, "Kai ma haka!" Bakin su ya hada, ya fara bara wani irin zazzafan kiss. Sai da yayi iya yin sa sannan ya dago ya ce, "Kece Farin cikina Husnah" Ido ta lumshe, tayi lamo a jikin sa. Ya ce, "Yau xamu samowa Nawal kani ko kanwa, tinda naga kamar tsarawa kike duk sai sunyu four to five years ko." Duka ta kai masa tana shigewa jikin sa. Nan ya shiga ga nuna mata zallar so. *ALHAMDULILAH *Dukkan godiya sun tabbata ga Allah da ya bani ikon rubuta wannan littafin lafiya. Ina kara godiya ga Allah.* Duk abinda na rubuta ba dai dai ba Allah ubangiji ya yafe mun. Wanda na rubuta dai dai Allah ya bamu lada baki dayan mu. Ameen Ina godiya gareki Mahaifiya ta abar alfahari. Wannan littafin kacokan naki ne, uwa ta gari. *Mahaifiyatah* Banda kamarki a duniyarnan, Allah ya barni dake ya kuma kara miki tsawancin kwana, Allah ya biyaki ya saka miki da gidan Aljanna. *Ameen* *Mahaifinah* Allah ya kara haskaka kabarinka mahaifina, Ya sadaka da rahamarsa *Ameen* *Kannenah* Abin alfahari na. Allah ubangiji ya muku albarka. Allah ya kara mana zumunci. *Ameen* *My Nusy and Yasmeen (Autah)* *Anty nah* Anty Rash ina godiya gareki. Godiya ta baza ta taba karewa a gareki ba. Ke daban ce. Allah ubangiji ya saka miki da mafificin alheri. Allah karawa iyayen ki lafiya da nisan kwana. Allah kawo miji na gari. Allah baki zuri'a daiyiba. *Ameen* soyayyar ki ta daban ce a cikin zuciyata. Allah ya bar mana zumunci. *Ameen* *Hajiya Nafisa,* Maman mu maganin kukan mu Allah ya ja da rai Ya raya zuria *Ameen* *My Barrister* Barrister Sady. Nagode sosai jin jina gareki. Allah ubangiji ya bar zumunci Allah ya biya miki dukkan bukatun ki na alheri. *Ameen* *HAJOW* *Hakuri da juriya Online writer's* Hajiya Nafisa (Momyn mu) Alawiyya Ado (Antyn mu) Sadiya Mohd (My Barrister) Fatima Mohd Kibiya (Sisinah) Maryam Ipteen (My swt Namesake) Maryam kabir Bako (My sis) Aina'u Gyaranya (Anty nahh) Hauwa Mohd (My slimsmall) Rukayya Zubair (Rukkybae) Maryam Aliyu (My Namesake love) Sumaiyya secret writer (sisinah) Rukayya Isa Nusaiiba Ummu Aysh Amina Abdulmajeed (Mamah nah) Sadiya Alhassan Ummu Affan Hindatu Sadiza Sardauna Ameerah Gwadabe dukkan ku ina kaunar ku Allah yabar zununci ina yin ku. Allah kara basira Ameen. *Sauran marubuta* Ina kaunar ku gaba daya. Allah ya kara mana hadin kai basira da ilimi. *Ameen* Na gaishe ku. *Masoya nah* A koda yaushe ina godewa Allah da ya bani masoya kamar ku. Banda bakin godiya sai dai ina muku fatan alheri kamar yadda kuke sona da littafai na da labarai na nima ina son ku gaba daya. Allah ubangiji ya sada mu a gidan Aljjana. Kuna da yawa sosai. Amman bazan manta da ku ba yan *INDABAWA HAUSA NOVEL* *HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITTERS* *RASH KARDAM HAUSA NOVEL 1 & 2* *RAZ NOVELLA* *DOKIN KARFE WRITTERS FANS* *KHALEESAT HAIDAR FCBUK* *ZAMA NA AMANA 2* *MARYAM SALISU MAI DALA* *INA ZAKI DAMU FANS* *SURAIYYAHMS FANS* *ZEE MAKAWA NOVEL 2* *HAUSA NOVEL* *KASAITUTUN MATA* *MARAHMAD CHATTING* *ZUWAIRAT NOVEL FANS* DA SAURAN SU DAI. Ummu Ayda, Bela'u, Fatitih, Aina'u, My sisto Kibdiyya, Hannatu, Mrs Arab, bbb, Zahra da duk yan Facebook gaba dayan ku masoya littafai na da kin comment da masu like. Haka nan yan wattapad masu voting suma ina godiya gare su. Masu karantawa ba vote kuma duk nagode. *KAWAYE NAH* A koda yaushe kuna raina. Nagode da kwarin gwiwar da kuke bani Allah ya bar mu har a gidan Aljamna tare *Ameen* A koda yaushe kece farko ko a ina ma haka a zzuciya ta. Hauwa kamilu Zimit (Mrs Bashir) Allah bar kauna Ameen. Zainab Umar Kunya (Kunya) Rabi'at shuaib idiris (Rabrah) Khadija Taiywh Na'abba (Taiyeb) Aisha Shuaib Hussain (My Asha) Rukayya Muhammad Abdullah (Kawata) Amina Ibrahim Adam (Mamanah) Halima Abdusamad Muktar (Sadiya) Aisha Mika'il Amina Sabo (Meenaroshan) Naima Aminu Barde (Barade) Nusaiba Khalit (Nusysy) Maryam Aliyu Yakasai (Merrymoney) Zainab Ahmad ukasha a ko da yaushe kuna raina Allah yabbarmu tare Allah ya sada mu har a aljanna gaba dayan mu da daran da ban lissafo ba. Amrah A Mashi Princess Amrah jinjina gareki. Hauwa A Usman Jidda na gaishe ki Aisha A Bagudu Allah taimaka Zauwairt Isma'il Ummu Maryam Allah ya dafa. Zahra'u Muhammad Mahmud Surbajo ina kaunar ki Allah ya dafa. SuraiyyahMS Ina kaunar ki. Allah dafa Zainab Makawa Allah ya taimaka. Da gaba daya Writer's ina kaunar ku gaba dayan ku. Daga marubuciyar 1)NI DA YAA MUSTY 2)MIJIN UMMUNAH 3)NAJWA 4)KOMA KAN MASHEKIYYA 5)ASMA'U HUSNAH *SAI MUN HADU A CIKIN SABON LITTFI NAH* *WANDA NA BATA WA YA YAFE MIN NI NA YAFE WA KOWA.* *FATAN ALHERI DAGA YAR MUTAN INDABAWA MARYAM SULEIMAN HARUNA INDABAWA (ANTTY)* MANS NAGODE LOVE U ALL