*Y'AR GARUWA........* _{ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ ơʄ ąmąʑıŋɠ wąɬɛr ۷ɛŋɖơr women}._ *STORY,WRITTEN & EDITING* *BY* _HAWWA M.U {®ɛąl $mąʂɧɛr}._ *COPIED BY.* _HAWWA M.U (REAL $MASHER)._  💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *8/mąrcɧ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *Da ѕυnayen υвangιjιnмυ tsarkaka naĸe ғara rυвυтa wnn laвarι, wanda ѕнι ya вanι daмa,laғιya,тare da вaιwar da a ĸυllυм nake godiya gareshi....* *Aminci,tsira su k'ara tabbata ga fiyayyen halitta,Annabi Muhammad (S.A.W) tare da ahalinsa da sahabbansa da wad'anda suka biyosu da kyautatawa har i zuwa ranar sakamako....* *~___________________________~* *wannan laвarι ĸ'ιĸ'ιrarѕa nayι,ѕaι daι yana d'auke da darussan rayuwa iri²,ina fata Allah ya bani ikon kammalawa lafiya....* *ban yarda a juyamin labariba ta kowace fuska,wanda yayi haka na barshi da Allah...* *Idan kunga kuskure aciki ina fata za kumin uzuri,Allah ya yafe mana baki d'aya, wanda yaga wani abu da yayi dai² da rayuwarsa yamin uzuri badon cin fuska nayi ba....* *Allah yasa mu dace.... Ameen thumma ameen...* *~___________________________~* _YA ALLAH INA ROK'ONKA DA SUNAYENKA TSARKAKA KA BAWA MAHAIFANMU LAFIYA,INGANTACCIYA MAI 'DOREWA,KAJI K'ANSU,KAYI MUSU RAHAMA......._ _WANNAN LITTAFI NA SADAUKAR DASHI GA MAHAIFANMU,NA GIDA DANA ASUBITI......._ *_•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°_* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *0⃣1⃣* *S*allama take tayi tun daga k'ofar gidan,amma ko tari ba ayiba,ga rana dake dukan kanta... Banda maik'o babu abunda take,jin ank'i ansawa,yasa ta d'aga allonta dake hannunta ta d'ora akanta,don kare ranar da ta addabeta... Zuwa can ta sake maimaita yin sallamar,nanma dai shiru aka mata babu amsa.... Hakan ne yasata tsugunawa,ta cire silifanta ta zauna akai kamar mai d'aukan darasi..... Tun daga nesa dattijon dake tahowa,yake kallonta,sauri ya K'arawa k'afarsa dan tabbatar da zatonsa.... Daf da ita ya k'araso,tare da fad'in *"NANA KHADIJATU*, Uwata me kikeyi a cikin wannan ranar da kowa yake gudunta???" 'Dagowa tayi da saurinta jin muryan mahaifinta dake tsaye,da murnarta ta kalli mahaifin nata tana fad'in "Abba na dawo ina sallama,ba a amsaba shi yasa na zauna anan ban saniba ko ba kowa a gida".... Banda abunki kuma uwata sai kizo cikin wannan ranar ki zauna kamar an miki dole... "Tashi maza mu shiga ciki,kar kuma ki sake zuwa ki zauna kinji ko,wannan ai sai wani ciwon ya kamaki"... Fad'in abban *KHADIJATUL KHUBRA*..... Hannunta ya kama suka kama hanyar shiga gidan.... Tun daga bakin k'ofar gidan yayi sallama,jin shiru ba a amsaba,yasa abban yaci gaba da kutsa kai cikin gidan had'e da sake yin wata sallamar.... Abunda ya matuk'ar bawa abba mamaki bai wuce ganin da mutum a tsakar gidanba..... K'arasawa yayi yana k'are mata kallo,kafin ya iya furta ‘’ladiyo dama kina zaune muke sallama,amma amsawa ta gagareki‘’..... Fuska ta yatsina (tamkar kayan miyan da yaso lalacewa)..... kafin ta bashi amsa da cewa ‘’ina ji sai me?? ko kuwa cewa akayi an ajiyeni ne dan na amsa muku sallama?''...... Ganin zata kunyata shi gaban y'arsa yasa yabar maganar ta hanyar fad'in ''Allah ya kyauta''...... Bud'ar bakin ladiyo sai cewa tayi ''ya kyauta abinda yafi haka''..... Bai kuma tanka mataba,ya juya yana girgiza kai,ya shige d'akinsa..... Duk wannan budurin da ake a gaban KUBRA ake,kanta na k'asa sai hawaye dake tsiyayowa daga ciki...... Ganin abbanta ya bar gurin itama ta juya da niyyar barin gurin.... Sai dai muryar ladiyo ta rigata k'arasawa bakin k'ofar d'akin,ta hanyar mako mata mula²n zagi...... Da sauri ta k'arasa shigewa,gabanta na dukan 9².... Can ku'ryar D'akin ta nemi guri ta zauna,tana jiran gawon shanu.... Cikin d'akin da baida wadataccen haske,take zaune,tayi shiru sai kalle² take tamkar wata bak'uwa,ko wacce ta fara rayuwa inda bata saniba,haka taketa fama ita kad'ai,a haka bacci yayi awon gaba da ita....... Wani k'ayataccen guri ta hango mai kyan gaske.... Sauri take ta k'arasa gurin,amma duk da haka ta kasa k'arasawa gurin,saima gajiya da tayi...... Haka ne yasata neman guri ta zauna,tana k'arewa gurin kallo ko zata hango inda ruwa yake..... Rashin ganin alamar ruwa yasata,juyawa ta kalli hanyar da ta biyo..... hanyace mik'ak'kiya wacce ko farkonta bata ganiba,bare k'arshenta,hakan yasata kifa kanta ta fara rera kukan rashin Madafa.... Tun daga nesa ta fara jiyo hayaniyar mutane had'e da wani daddad'an k'amshi da yasata saurin d'ago kai,tana bin hanyar da hancinta..... Ayarine na mutane da suke da mayuk'ar yawa suke shirin giftawa ta kusa da ita...... Da sauri ta mik'e tabisu duk da suna kan abun hawa,hakan bai hanata shiga gabansuba,tana fad'in "Dan Allah ku taimakamin".... Babu wanda ya saurareta,sai zagayeta da sukayi suka ci gaba da tafiya...... Da gudu² ta sake shiga gabansu,tana rok'onsu..... Wannan karon kam saboda haushi da ta bawa wasu daga cikinsu yasa su yi mata tsawa.... A firgice,jikinta har rawa yake saboda tsoro take kallonsu,wani k'ato da yayiwo kanta d'auke da bulala yasata fara kuka.... tana bashi hak'uri,d'aga bulalar ya d'aga da niyyar sauke mata a jikinta...... Kafin ya k'arasa ida nufinsa,wata siririyar murya daga bayansa take fad'in kada ka kuskura ka aikata abunda kake k'ok'arin yi ..... Da hanzarinsa ya juya don ganin mai magana,sai dai ganin fuskar wanda yayi maganar yasa shi kaucewa daga kusa da ita,jikinsa na kad'awa tamkar Mazari....... Kyakykyawan matashi ne ya bayyana daga inda ya kauce,yana sanye cikin fararen tufafi,tafiyarsa cike da k'asaita,har ya k'araso Inda suke..... Kallon k'aton yayi kafin ya bud'e baki,har ya rigashi cikin ladabi da girmamawa yake fad'in ''tuba nake ranka ya dad'e''...... Hannu ya d'aga masa,ba tare da ya sake yunk'urin yin maganaba,ya juya da nufin barin gurin............ *~_KEEP MOVING 😍😍😍……………_~* *_REAL SMASHER 🤞🏻😘.._* 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *9/mąrcɧ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *__________________________* _Godiya gareki *FATEEY TAMBARIY* tabbas y'an *TIME WRITER'S* muna godiya marar adadi gareki,Allah ya kara baseera,hazaka da kuma daukaka..._ _Ki jima kiyi karko tawan,Allah ya bar zumunci da kauna..._ *__________________________* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *0⃣2⃣* *C*ikin sauri tabi bayansa,tana k`ok`arin tsayar da shi,sai dai hak`anta bai cimma ruwaba….... Duk da bawai sauri yakeba,haka take binsa tana fad`in *"BAWAN ALLAH* ka tsaya"...... Ganin ta kasa cimmasa,kuma baiyi kokarin tsayawaba,yasa taci gaba da binsa.... Sai dai kamar wanda yake tafiya a cikin iska,haka ta kasa riskarsa,tsayawa tayi,lokacin ne ta hangoshi har ya dad`a mata nisa sosai..… Zama tayi cike da takaici,gashi ko sunansa bata saniba,a matsayinsa na wanda ya ceci rayuwarta..… Murmushi ta saki lokacin data tuna cewar zasu sake had'uwa koba wannan lokacinba....… *************** *LADIYO* dake zaune tsakar gida,wadda tun wucewar *KHUBRA*,take rafka mata kira...… Jin shiru babu amsa yasata mikewa tayi hanyar d'akin,da niyyar dubawa taga uban me take da har zata kirata tak'i amsawa...… Shigarta d'akin ta tarar da ida kwance kan dagargazajjiyar tabarmarta,da take kwana kai..…… Ganinta tana bacci ba k'aramin b'acin rai tajiba,Kai ta girgiza,kafin ta koma da baya,tana fad'in da ni kike zancen yarinya...… K'aton randan k'asa ta d'auka,ta nufi d'akin dashi,bata jira komaiba,ta juyeshi akan *KHUBRA* dake tsaka da dreaming....… **************** A razane ta mik'e tana duba jikinta da yayi sharkaf da ruwa ga shi duk d'akin ya jik'e ruwan har ya kwanta,a tsakar d'akin...… 'Dagowa tayi ta kalli *LADIYO* dake tsaye tana watsa mata wani mugun kallo...… Sake juyawa tayi ta kalli d'akin duk wani kaya dake ciki a jik'e yake,saboda ruwan ba kad'an bane...… Kayanta ta fara tattarawa da niyyar gyarawa...… *LADIYO* dake tsaye,tana raba ido akanta,ta fizgota tare da wanke mata fuska da mari...… Gigicewa *KHUBRA* tayi,ta rasa me zatayi,shin kuka za tayi ko kuwa me???? Rashin madafa yasata neman hanyar ficewa daga d'akin...… Ashar en da *LADIYO* tayi ne ya dakatar da ita,juyowa tayi,cikin ladabi tana fadin "Kiyi hakuri baba ladiyo,zan gyara gurin ne"………… ''Dan ubanki ni kike fad'awa zaki gyara guri,to billahillaziy baki isaba'' fad'in LADIYO kenan kafin ta d'ora da cewa...... ''Maza tun kafin na sab'a miki,ki wuce ki d'ebo ruwa,kin san aiki na nan yana jiranki,kika shigo d'aki kika kwanta ke ga sarauniya koh?''...... Rab'awa tayi ta kusa da ita ta fice,ba tare da ta sake cewa komaiba,sanin irin aikin dake gabanta..... Tulunta ta d'auka ta kama hanyan rafi,jikinta duk babu dad'i ga kayanta dake jik'e....... Tafiya take duk kunya ya isheta,saboda surar jikinta dake bayyane ta jikin kayan,duk da bawai banyan ne yake da mutaneba,sai dan kasancewarta mace mai tsanin kunya...... Tana tafe tana tunanin abunda ya faru yanzun,kafin fitowarta daga gida..... A wani b'arin kuma na zuciyarta tana tunanin mafarkinta,Wanda shi ne kusan zata iya sashi a matsayin silar faruwar komai....... A haka ta kammala d'iban ruwa,ta sake duk'ufa kan aikin cikin gida,duk da kasancewarta ba mai yawan shekaruba,amma yau da gobe yasata gogewa a fannin aikin gida...... Wuni guda tana aiki,tamkar jaka har kusan almuru ta kai,kafin ta kammala aikin....... Sai a lokacin ne ta samu kwanciyar hankali,bayan ta je ta watsa ruwa,alwala ta d'auro ta shige d'akinta,da tun fitarta bata sake samun damar komawa cikinsaba sai ynzn....... *************** Ta jima a tsaye tana kallon yadda k'asar gurin ta tsotse ruwan..... Haka ta lallab'a ta rab'a gefe ta kabbara sallah... Kafin wucewar wasu sa'o'i har ta idar.... Kwanciya tayi a gurin duk ta takure guri d'aya...... Sai a lokacin tunanin mafarkinta ya sake dawowa,murmushi tayi,tare da fatan sake ganin fuskarsa ko da a mafarkin ne,duk da dama bata tsammanin ganinsa a zahiri...... ************* Haka rayuwar *KHUBRA* taci gaba da kasancewa,kullum safiyar Allah za taje makarantar allo,daga zarar ta dawo kuma zata fad'a harkar aikace² har goshin maghreb..... Bata da wajen zuwa,kullum tana gida (kamar daddawa)....... Rayuwarta ita kad'ai,babu k'awaye,bare ta samu abokin shawara...... Babban damuwarta baya wuce rashin zuwa dangin mahaifiyarta,Wanda tun kafin ta girma,shima bawai zata iya tunawa bane..... Siraran hawayen da suka sakko mata ta goge,tare da tausayawa rayuwarta,irin k'angin da take ciki............ *_~KEEP MOVING..... 😍😍😍~_* *_REAL SMASHER 🤞🏻😘_* 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *10/mąrcɧ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~__________________________~* _Ina matuk'ar godiya da addu'anki gareni,ina kuma jinjina gareki bisa k'ok'arinki Allah ya k'ara basira Doughteeyy *AISHA ISAH (MUMMY'S FRIEND)*......._ *~_#DUK WUYA MUNA TARE DA IZININ UBANGIJI.....~_* *~__________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *0⃣3⃣* *D*a sanyin safiyar wata laraba,tana tafe a hanya,tunanin mutumin da ta gani a mafarkinta ya sake dawo mata,ji tayi duk duniya babu abunda take da muradin gani sama da shi...... Wanda rabonta da shi tsawon sati guda kenan...... Sauri ta shiga yi na ganin ta k'arasa gida,burinta bai wuce tayi aikin da ta saba ta k'are ta kwanta ko zatayi dace a yau tayi katarin ganinsaba.... Da haka ta k'arasa,sai dai me zata tarar,zuwanta gidan ta tarar da LADIYO da wata k'anwarta da tazo daga garin KANO suna zaune cikin rumfa banda shewa babu abunda suke,duk sun cika gidan da hayaniya.... . Tayi sallama yafi a k'irga,amma cikinsu babu Wanda yayi yunk'urin amsawa.. Haka ta wuce ta ajiye allonta..... Dawowa tayi har k'asa ta durk'usa ta gaida ASMA'U wacce akema lak'ani da MA'U........ Yatsina fuska tayi,kafin ta kalleta had'e da zabga mata wata uwar harara........ Tsakine ya biyo baya,cikin tsawa take fad'in ''ke ni dallah b'acemin anan gurin,kinibabbiya kawai''..... Cikin sanyin jiki KHUBRA ta mik'e ta bar gurin,ranta duk a b'ace,haka ta Shiva aiki babu ji babu gani...... *°°°°°°°°°°°°°°°* LADIYO ce ta buga wani uban tsaki,da yasa k'anwarta MA'U kallonta,tana fad'in ''YAYA ince dai lafiya''....... ''Inafa lafiya,wannan shegiyar yarinya tana gidan nan ina naga kwanciyar hankali'',cewar LADIYO.......... Nan MA'U ta samu dama,ta fara magana da cewa ''YAYA aradu nu kaina na tsani tarinyar nan,da nazoma banyi tsammanin tana nanba,amma yanzun ga wata shawara....... Me zai hana ki bani ita mu tafi birni,a samamata aikatau,duk wata abunda aka biya sai ina aiko miki da shi,kinga kin huta zaman banzan nan,ke ba sana'aba,ko kuwa ya kikace?'' Ta k'are maganar tata da son jin amsar da za a bata....... Tunanin maganar MA'U ta shiga yi,zuwa can kuma ta ce ''To amma banda abinki MA'U ta ina zaki tafi da ita ba tare da ubanta ya saniba,ni da bani na haifetaba,dama anamin gorin ko kwai na kasa ajiyewa,kuma na tabbatar ba yarda zaiyiba''...... ''Haba YAYA ke kam kamar ba mace ba ko da yaushe aka kawo magana bakya saurin amincewa sai kin kawo suka,shi kenan kinga ai sai kiyi ta zama babu sana'a'' ta fad'a tana had'e fuska,da alama bata hi dad'in maganar da y'ar uwar tata ba........ A'a MA'U baki fahimci me nake nufiba,dolefa sai malam BUBA yasan inda zata,kodama ace an tafi da ita babu saninsa saiya tambaya,kuma yana ganin bani na haifetaba ta ina zai amince da abunda zan fad'a....... ''Shi kenan na gane,amma dai kisan yadda za kiyi ki had'a mata kayanta,a kaita aikatau kema kya samu kifi k'arfin wani abun''....... Yanzun an daina saka y'ay'a a gaba ana kallonsu,barema ke da babu d'a bare jika........ Ki lallab'ashi akan ni zaki bawa aronta,mijina ne baya nan zata tayani zama,zuwa nan da wani d'an lokaci zata dawo......... Kinga daga nan sai dai yaji kid'a a magwan....... Nan suka sa shewa,har da tafawa....... Wunin ranar haka MA'U ta zauna tanata yiwa LADIYO hud'uba,wanda k'arshe sai da ta amince,akan ko Malam en baya so sai ta aikata........ *°°°°°°°°°°°°°°°* Kwanakin MA'U uku a k'auyen na KASHIN DILA,tayi niyyar komawa inda ta fito....... Kayan da KHUBRA ta fito da shi ne ya tabbatarmin da sunyi nasara akan k'udurinsu...... Fuskanta cike da damuwa,haka sukayi sallama,har bakin k'ofar gida LADIYO ta rakosu,tana yiwa y'ar uwarta fatan sauka lafiya...... Nan suka kama hanyan barin garin,mashin d'in achab'a suka hau,daga nan bai saukesu ko inaba sai tashar garin na HAD'EJIA........ Misalin k'arfe d'aya na rana motarsu ta harba kan titi....... *~#SAFE TRIP KHUBRA...~* Tafiya ta mik'a,inda KHUBRA dake cikin booth,tsakiyan kaya,tunanin abun duniya duk ya isheta,tana ta sak'a da war-wara bata san lokacin da bacci yayi gaba da itaba....... *°°°°°°°°°°°°°°°* Juyowa yayi ya hangota durk'ushe ta kifa kanta,banda kuka babu abunda take...... Cikin takunsa na k'asaita ya k'araso har gabanta...... Bata san zuwansaba,sai k'amshinsa da ta jiyo daf da ita..... Cikin hanzari ta d'ago,baki ta bud'e da niyyar magana....... Hannu ya mik'a ya rufe mata bakin,nan KHUBRA ta zaro ido,ganin abunda yake faruwa..... Da sauri ta cire hannun nasa daga bakinta,cikin damuwa take fad'in ''Me yasa zaka tab'ani bayan ni ba muharramarka bace?''....... Kallonta yayi tun daga sama har k'asa kafin ya iya bata amsa ''Kin tab'a jin inda akace idan miji ya tab'a matarsa yayi laifi?''...... "Bud'e baki tayi tana k'are masa kallo,ta ina na zama matarsa?" Abunda KHUBRA bata saniba a fili tayi maganar....... Cikin b'acin rai da fushi ya fara magana ''Nayi miki k'arya kenan? tunda kin d'aukeni a mak'aryaci,daga yau bazaki sake ganina ba,zanyi nisa da ke,har zuwa lokacin da zaki fuskanci gaskiya'' Daga haka bai sake yi mata magana ba ya juya yaci gaba da tafiya......... Hak'uri take bashi akan ya dawo,amma ina haka duk kukan da take bai koda sake waiwayeba....... Kuka mai tsanani ta keyi,tana fad'in dan Allah karka tafi ka barni,ka dawo dan Allah na yarda............ *°°°°°°°°°°°°°°°* Dai² lokacin da take tsaka da dreaming,suka k'araso birnin KANON DABO gari mai tarin albarka....... Baccinta take shak'a a Booth sai bakinta dake motsi tana juya kai,hawaye sai layi yake akan face enta...... Har aka bud'e booth en bata saniba,sai da MA'U ta k'araso gurin tana masifar rashin fitowar KHUBRA nan ta tarar da ita tana bacci,mari ta zabga mata,a firgice ta tashi,tana dafe da kuncinta,ta sakko ta shiga jidar kayan,suka kama banyan fita daga tashar....... Sai lokacin ta tabbatar da cewa abunda ya faru duk mafarki ne..... fuskanta ta shafa,ruwan da taji ta gogo yasata mamakin inda ta sameshi....... Dallah ni kina b'atamin lokaci,kin wuce mun tafi ko saina zane miki jiki......... Cikin sanyin jiki ta ja k'afafuwanta suka ci gaba da tafiya........... *_~KEEP MOVING.... 😍😍😍~_* *_REAL SMASHER 🤞🏻😘_* 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *20/mąrcɧ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~__________________________~* _Ina mai baku hak'uri na rashin jina da bakuyi,duk da wasu sunsan uzurina na rashin mahaifina da nayi a safiyar litinin, *12/03/2018* ina fatan zaku tayani addu'ar samun dacewa da rahama a gareshi da sauran al'ummar musulmi baki d'aya, rayayyu daga ciki da kuma matattu,Allah yasa muyi kyakykyawan k'arshe......_ *AMEEN...* *~__________________________~* *_INNALILLAHI MAA AKHAZA WALAHU MAA A'A'DA WA KULLI SHAI'IN INDAHU BI AJALIN MUSAMMA FAL TASBER WAL TAHTATHEEB..._* _Ya Allah Kaine mafi sani da abunda ke b'oye,na zahiri,Wanda zai faru gaba,da Wanda ya faru a baya,Allah kayiwa mahaifanmu rahama,gafara,afuwa,ka sadasu da rahamarka......Ameen thumma ameen._ *~_________________________~* _Ya Allah ina rok'onka da sunayenka tsarkaka,Allah ka dubi halin da y'ar uwata take ciki,ka bata lafiya,ingantacciya mai d'orewa,Allah ka tashi kafad'unta....._ _Wish u a very quick and speed recovery *MY SISI HUBBEEY.*_ 💔 *~_________________________~* _Kun nunamin karamci a rayuwa,soyyaya,k'auna,Wanda baki ba zai iya jurar furta kalamai garekuba,hak'ik'a ku en masoyane na asali,ubangiji ya biyaku da mafificin alkhairinsa..._ *ONLINE WRITER'S TARE DA READER'S* daga ko wane gida,ina alfahari da kasancewa tare da ku,ina jinjina gareku musamman wad'anda ke cikin wad'annan gidaje....._ *SMASHER & HUBBEY NOVEL GROUP.* 💔❣ *REAL SMASHER NOVELLA GROUP.* 💔❤💘 *A LAUNI HAUSA NOVEL.*💞 *TIME WRITER'S.* 🕙 *WRITER'S ONLY.* 📚📝 *RAYUWAR BASMA.* 🌹 *WRITER'S VILLAH.* 😘😍 *MUSAN JUNA ONLINE WRITER'S.* 💃🏻🤝🏻 *KANAWAN DABO WRITER'S ROOM.* 🤝🏻 *OUR LADIES OUR PRIDE.* ❤ *PRECIOUS FAMILY.* 👨‍👩‍👧‍👦 *BA NI NAYI KAINABA FAN'S.* 💖 _Ina godiya sosai,wacce bata da limit a zuciyana,bisa ta'aziyyan mahaifina,Allah ya bar k'auna..._ *~__________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *0⃣4⃣* *T*afiya kawai suke ba tare da *KHUBRA* ta san inda suke nufaba,sai kalle² take a haka har suka fito bakin hanya... Kafi babur suka tare,MA'U ta tak'ark'are ta hau yi masa bayanin rijiyar lemo zai kaisu...... Kud'in da ya yanko mata zata bayar,ta tsaya wangale da baki,nanfa suka tsaya ciniki,yi take kamar ba za a dainaba,d'an adaidata da yaga bazai iyaba,yaja kekensa yayi gaba..... Duk Wanda za ta tsayar idan taji bai mata yanda take soba sai dai yaja Babur ensa ya k'ara gaba....... Son kud'i irin nata ya hana su tafiya....... Sun jima tsaye ba tare da sun samu abun hawaba..... Ita MA'U son kud'inta da ganin tsada ya hanata ta biya akaisu inda zasu..... Haka sukaci gaba da jira,yamma na dad'a kunno kai...... 'Bangaren KHUBRA kuwa wata azababbiyar yunwace tafi addabarta ga bakinta da ya bushe saboda tsabar k'ishi da ya dameta..... Rashin sanin abunyi da kuma hali irin na MA'U yasa ta ja bakinta tayi shiru,sai raba ido da take akan hanya...... Ganin tsaiwa bazai kai musuba,da kyashin biyan kud'in motar yasa MA'U juyawa ta kalli KHUBRA,tana yatsina mummunar fuskarta...... Tunda nake a rayuwata ban ta'ba zuwa na b'ata lokaci a tsaye ba tare da samun abun hawaba sai yau da na d'auko MAI BAK'IN JINI...... Jin furucinta na k'arshe yasa jikin KHUBRA dad'a yin sanyi.... Ba tare da ta kalletaba,haka bata ce uffanba....... ''Yanda kikaimin bak'in ciki na rasa abun hawa haka wallahi saina fanshe kud'ina tare da ke MATSIYACIYA Y'AR MATSIYACI''....... Maganan da ya fito daga bakin MA'U kenan wanda ba k'aramin sosawa KHUBRA rai yayi ba,take hawayen da bata son fitowansa ya b'alle,ita kam da ita ta zaga babu da zai sa ta damu,abunda yafi komai bak'anta mata rai zagin ABBANTA da MA'U tayi.... Ko ganin girmansa batayiba,bare d'aga masa k'afa a matsayinsa na miji ga yayarta....... Wannan shi ne abunda ya jawo mata ZUBAR HAWAYE..... Dad'a sunkui da kanta tayi k'asa,ta shiga goge face nata,dan ta tattabata idan MA'U ta san halin da take ciki tana mai iya jibgarta a gurin tamkar kayan wanki...... Sake tsaida wani tayi,babu ko ciniki ta afka tare da cewa ''idan kinga dama kya taho mu tafi..... Jan k'afafunta tayi ta shiga,duk da haka bata tsiraba,k'arshema sai cikin booth d'in mashin en ta zauna,tun daga kasuwar ta y'an kaba har zuwa unguwan na rijiyar lemo...... ************** Sun is a unguwan ana sallan Maghreb,yana saukesu ta laluba cikin d'an topinta ta zaro masa kud'insa.... Kud'i sosai KHUBRA ta gani ta fito da shi,nan ta tabbatar matar tana da bak'in hali.... Tunani ta shiga yi,na irin rayuwar da zata fuskanta nan gaba,ko yaya zata kaya tsakaninta da MA'U?........ *_Ni ko nace ai KHUBRA bakiga komaiba......._* *_~Kumin uzuri fan's in sha Allah next page zaizo ba kamar wannan ba..... ~_* *_Masoya novel ena na RAYUWAR WANI kuyi hak'uri na jina shiru kwana biyu in sha Allah zanci gaba daga inda na tsaya,na gode sosai_* *_~IYA WUYA MUNA TARE......~_* *_~KEEP MOVING.....~_* 😍😍😍 *_REAL SMASHER 🤞🏻😘_* 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *21/mąrcɧ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~__________________________~* *ADDU'AH KAN ABOKIN GABA...* _ALLAHUMMA ANTA ADHUDHIY,WA-ANTA NASIYRIY,BIKA AHULU,WA-BIKA ASUULU,WA-BIKA UK'ATILU......_ _ALLAHUMMA INNA NAJ'ALUKA FIY NUHURIHIM,WANA-UZHUBIKA MIN SHURIRIHEEM......_ *_~#HISNUL MUSLIM....~_* *~__________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~__________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *0⃣5⃣* *B*inta kawai KHUBRA take a baya² har suka k'arasa k'ofar gidan..... Mukulli ta zaro irin wanda ake kira da (KUBA) en nan ta shiga murd'awa a jikin k'ofan,da kyar ta samu ta bud'e saboda taurin da k'ofan yayi..... Gidan bak'i k'irin da shi,ga uban daud'a da yayi,kai saika rantse bai tab'a ganin wani abu mai kama da tsintsiyaba..... Kunna kai tayi ciki ba tare da ta damu da addu'ar shiga gida ba,duk dama dai bana tunanin ta iyata.... KHUBRA dake baya,ta tsaya k'ofar gidan kafin ta shigo.... Sai da tayi addu'ah ta sanya k'afanta cikin gidan,kasancewar mahaifinta yana koyar da ita ilimin FIQHU,AZKAR da sauran abunda ba a rasa ba na zamantakewar duniya...... Bata tarar da MA'U a tsakar gidanba,guri ta samu ta zauna gudun kada tayi laifi,coz ta san yanzun sai ta bi a hankali,tunda tasan halinsu ba k'aunarta sukeba...... Tayi nisa cikin tunani,kan mafarkinta... Abunda take son fuskanta kan mafarkin ya gazawa tunaninta.... Tashi tayi tana k'ok'arin shiga band'aki danta samu ta rama sallolin da ke kanta,nan ta bar kayan ta shige..... Ko uzurin da ya kaita bata k'arasaba ta tsinkayo muryan MA'U daga tsakar gida tana surfawa iyayenta zagi.... K'irjinta ta dafe had'e da zaro ido,dan ko ba a fad'a mataba tasan laifinta..... Addu'ah ta hau yi a zuciyanta,tana me neman tsarin ubangiji tsakaninta da MA'U da kuma zaman da zasuyi nan gaba...... Fitowanta ta tarar da ita tsaye ta rik'e k'ugu kamar wata k'aramar yarinya sai girgiza take..... Kallo d'aya ta mata ta d'auke idonta a kanta,ta sunkuya ta fara alwala...... ''Don ubanki ni zaki mayar mahaukaciya ina magana ki juyamin baya,ko ubanki wannan matsiyacin bai isaba wllh''... Maganar da ta biyo bayan hucin da take kenan kamar wata KUMURCIN MACIJI....... K'in magana,duk da kalmomin da tayi amfani dasu sun shigeta,shiru tayi har sai da ta idar da alwalan,sannan ta juya tana bata hak'uri...... Wata uwar harara ta rakata da shi kafin ta figi kayanta tayi cikin d'aki....... Gajiya da tayi da tsaiwa,ganin ank'i kulata bare ta samu a kirata,kan dole ta nufi hanyan d'akin bakinta na d'auke da addu'ah.... A kwance ta tarar da MA'U,nan ta tsaya tunanin koh wane hali mahaifinta yake ciki a yanzun...... Tsayawan mutum MA'U ta gani kanta cikin sauri ta bud'e idonta,tana zabga mata harara.... Kame² KHUBRA ta fara kafin da kyar ta iya furta ''Dama abun sallah nake so''... Bata tanka mataba,haka bata tashi ba,saima dad'a rufe idonta da tayi,tana daga kwance kan gadon k'arfe irin na da ennan..... Ganin tsaiwa bazai kai mataba,ta kabbara sallah daga inda take tsaye..... Tana sallah tana dafe cikinta da yake ihun yunwa,a haka har ta samu ta idar ba tare da ta kai GA fad'uwaba..... MA'U kam bacci ne ya kwasheta nan,ba tare da tunanin tashi ta gaida mahaliccinta ba..... Har bacci ya fara d'aukanta ta tuna da k'ullin kayanta dake waje,cikin hanzari ta fita ta d'auko bata dawo d'akin ba saida ta tabbata ta kulle k'ofar gidan..... 'Dakin ta dawo ta hau bud'ewa,can k'asan kayan ta binciko wani k'ullin leda da ABBANTA ya bata tun jiya.... Bud'ewa ta hau yi,k'uli² ne mai d'an yawa irin wanda ake yinsa da sugar ennan..... Ci ta fara,kamar wacce ta samu nama,haka ta far masa,sai da taci mai yawa,sannan ta hak'ura ta d'aure ta mayar cikin ledan...... Waje ta sake komawa cikin randa ta d'ebi ruwan da tasan zata iya shanyewa.... Godiya tayiwa Allah,sannan ta koma d'akin ta kwanta a k'asa dai² inda ta idar da sallah..... Take kuwa bacci yayi gaba da ita...... ************ Daf da kiran sallan assalatu ta farka,kasancewar ABBANTA kullum shi yake tashinta idan zashi masallaci sallah da asuba.... Fita tayi ta d'auro alwala,tsakar gidan da duhu sosai,haka ta daurewa zuciyarta tayi sauri ta dawo d'akin....... Har ta idar da sallan MA'U ko juyin farko batayiba,haka itama KHUBRA batayi gangancin tashintaba..... Gefe ta koma,ta had'a kai da gwiwa,tana tunanin duniya da makomar zuwanta wannan gari,tasan dai babu komai cikinsa face zallar wahala...... Ganin tunani ba kaimata zai ba,ta shiga karanta AZKAR na safiya,tana zaune har gari ya k'arasa wayewa...... Hijab dake jikinta ta cire ta fita tsakar gida...... Tsintsiya ta d'auka ta hau shara,kafin wani dogon lokaci har ta kammala,sai ga gidan yayi haske daga bak'ar daud'ar da yayi..... Har tayi wanka MA'U bata san me yake faruwaba... 'Dakin ta dawo,da tunanin ta tasheta ko kuwa...... Tsayawa tayi tana nazarin ta inda zata fara,amma fargaba ya hanata tab'uka komai..... Kan dole ta hak'ura,ta zubawa sarautar Allah ido...... ************* Sai misalin k'arfe 8:00am ta farka tana ta faman zabga hamma,had'e da mik'a.... Da kyar ta iya tashi tayi waje,ganin tsakar gidan a share tas,ta tab'e baki,ta rarumi buta tayi band'aki,ta jima aciki,tamkar wacce ta sami d'aki,zuwa can kuma ta fito,ta sake d'iban ruwa a bokiti ta koma.... K'arar ruwa kawai kake ji kamar wacce taje suuuu kogi,haka ta shek'ashi a jikinta ta fito,cikin abunda bai wuce minti 5 ba....... Alwalan ma buji² akayi aka fad'a d'akin..... Shigarta ta tarar da KHUBRA har ta gyara d'akin tsaf duk ta gyare tarkacen dake cikin d'akin..... Babu ko sannu bare an gode,saima ladan gaben harara da yatsina da ta shiga yi...... Shiryawa tayi cikin gaggawa,tasa wata atamfa riga da zani,taja gazal a idonta...... Takalminta ta sharfad'a tayi waje ba tare da yin ko da sallan da akayi alwala domin taba...... Babu magana bare KHUBRA ta sa ran ganin abinci tayi waje,tana gaisheta ma ko ta kanta bata biba..... Ta k'arawa k'afafuwanta mai....... *_~ALLAH YA SHIRYA.......~_* *_~KEEP MOVING....~_* 😍😍😍 *_REAL SMASHER🤞🏻😘_* 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *22/mąrcɧ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~__________________________~* 🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾 *APPY APPY BUFDAY* _Hope your birthday blossoms into lots of dreams come true! May today be filled with laughter and love._ _Happy Birthday and many happy returns of the day._ 🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂🍾🎂 *HAPPY BITHDAY 2 U!!* H B Z A U Y A B A A T B I R A *(YAYA HAYAT) ADMIN OF ADMINS.......* _Wannan ranar taka ce,babban Admin mai kundin novels, *WRITER'S* naka *REDER'S* naka,kana k'ok'aree gurin nishad'antar da d'aukacin members enka dake cikin_ *COOL NOVELS GROUP'S 1,2,3,4 & 5, MAKEUP ND KITCHEN GROUP* _Allah ya k'ara 'daukaka,ya k'aro maka shekaru masu albarka,kana mai wadatuwa da imani,kwanciyar hankali........_ _Wannan page en naka ne kai d'aya kayi yadda kaso da shi....._ ✍🏻✍🏻 🍾🍾🎂 *HAPPY BUFDAY WULLNUP ADMIN...* 🎂🍾🍾 *~__________________________~* *ADDU'AH YAYIN TASHI DAGA BACCI* _ALHAMDULILLAHIL-LAZIY AHYANA BA'ADA MAA AMATANA WA-ILAIHIN-NUSHUUR..._ _ALHAMDULILLAHIL-LAZIY AFANIY FII JASADIY WARADDA ALAIYYA RUHIY WA-AZINALIY BIZIKHRIY....._ *_~#HISNUL MUSLIM...~_* *~_________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~__________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *0⃣6⃣* *I*ta d'aya zaune tayi shiru,abun duniya duk ya taru ya mata yawa...... Tunanin gida da mahaifinta duk shi yafi damun zuciyanta,ko a wane yanayi yake? Allah shi ne masani...... Ganin babu sarki sai Allah,shi yasa ta bawa zuciyanta hak'uri...... 'Daki ta sake komawa,bayan ta tura k'ofan gida,da yake ta san ita kad'ai ke gidan,gudun kuma kada wani abu ya faru...... *********** Tafiya take duk inda ta samu watsa k'afafuwanta take,tamkar wacce zata tashi sama..... Son kud'i irin nata ya hanata neman abun hawa...... Sai da tsakiyan rana,ganin babu haza yasa ta hak'ura ta nemi keke napep,daga UNGUWAN KURNA zuwa RIJIYAR ZAKI,a ganinta nan ne unguwar masu kud'i,za tafi samun gidan aiki,idan bata samuba kuma,zuwa gobe sai ta nausa cikin gari...... Zafin rana da k'ishi su suka haddasa mata tsaiwa,ta nemi abun hawa,idan yaso sai ta k'arasa,in da ta nufa...... Ta tsayar da masu napep sama da guda goma,amma da sun tsaya suke k'arawa babur en nasu wuta suyi gaba....... Da kyar ta samu abun hawa,kan neman ragi irin na MA'U...... Yinin ranar yawo ta dungayi gida² take bi a unguwan na rijiyar zaki,kan neman gidan da suke neman Y'AR AIKI..... Sai da ta sha wahala,kafin ta samu gidan da suka nuna mata suna buk'ata...... Sun gama ciniki kan dubu biyar per month...... Duk iya yinta na su k'ara mata wani abu,hakan ya faskara.... Gudun kada tayi asara gashi wannan d'inma da kyar ta samu,bayan yini da tayi tana GARARIN DUNIYA yasa ta amince,akan zata kawota daga zaran sun gama shiryawa...... Abinci matar ta kawo mata da ruwa mai sanyi....... Ta gama d'amke cikinta,sannan tayi mata sallama........ Godiya tayi ta tafi da alk'awarin nan da Sati d'aya zata dawo...... *********** Kwance take tana ta faman bacci wanda bata san lokacin da ya d'auketaba,tayi nisa cikin baccinta....... ************** Tun daga nesa ta hango ingarman dokin wanda akewa lak'ani da KILI ( wato mai fari biyar),kansa mutum ne zaune,cikin farare tas en tufafi...... Matsowa yaci gaba da yi,wanda har sai da yazo daf da ita sannan ne ta iya gane mahayin murmushi d'auke kan fuskansa...... Sai da ya zo gabanta,sannan yaja linzamin dokin ya tsaya..... Har lokacin tana tsaye fuskanta cike da mamakin ganinsa...... Mutumin daya ce bazai sake dawowaba yau shi ne a gabanta yau....... Saukowa yayi cikin isa,ya tako har zuwa gabanta.... Cikin wani irin voice da bata tab'a jin irinsa ba tunda take a gaba d'aya tsawon rayuwanta,ta tsinkayo shi yana fad'in _''Amincin Allah yaci gaba da tabbata agareki''........_ Kasa amsawa tayi saboda tsananin mamaki da yak'i barinta har yanzun...... Hannunta ya kama cikin wani irin salo,ya jata jikinsa..... _''Haba wifey,ni en ne baki ganeba ko kuwa na zame miki wata sabuwar halitta?''......_ Kuka ne ya kufce mata,jikinta banda rawa babu abunda yake,tsabar tsoro ta kasa magana,sai hawaye dake ta ambaliya a fuskanta..... Duk k'ok'arinsa da son ganin ta bud'e baki tayi magana abun ya gagara...... Janta yayi ya had'a jikinsu guri d'aya,ganin yanda jikinta yake ta faman b'ari...... Maimakon a samu sauk'i saima k'aruwa da aka samu......... Kukantane ya sake tsananta,kan dole ya raba jikinta da nasa.... Fuskanta ya kama ya d'ago,tsura mata ido yayi _''Shin bakiyi farin ciki da ganinaba ne wifey?''...._ Kai ta girgiza masa,alaman A'a _''Baby maganafa zakiyi,bana son wannan nodding en''......_ Cikin hanzari ta bud'e baki da niyyan magana _''A'a,ina mamakin yanda ka dawo gareni ne,alokacin da bantab'a tsammaniba''........_ Fuskanta ya shiga goge mata,yana murmushin jin dad'i...... ********** k'afafuwanta tamkar wacce taje sharan gona,sunyi futu² kamar basu tab'a ganin mai ba....... Sai murna take na samun gidan aikin da tayi,haka ta sauka a napep en da ya sauketa bakin titi..... Ta sake ninkawa ta shiga cikin unguwan,a k'ofar gida taja burki,ganin k'ofan a rufe,ta shiga huci..... Bugun k'ofa ta shiga yi,jin shiru ba a bud'eba,ta shiga dukanta da k'arfi tamkar zata karya....... ************ Cikin baccinta mai dad'i mai cike da mafarkin da a kullum shi ne birinta.... Ta tsinkayo bugun k'ofan da tamkar a tsakiyan kanta ake...... Bud'e idonta tayi,cikin sauri ta mik'e ta nufi k'ofa,har tana had'awa da d'an gudu,wanda saura kad'an ta fad'i,amma haka ta daure ta tunkari k'ofan.......... *_~Uhmmmm ko me KHUBRA zata tarar yau kam.......~_* *_~KEEP MOVING...~_* 😍😍😍 *_REAL SMASHER 🤞🏻😘_* 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *23/mąrcɧ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~__________________________~* *ADDU'AR SANYA TUFAFI.* _________________________ _ALHAMDULILLAHIL-LAZIY KASANIY HAZAS-SAUBA,WARAZAK'ANIHI MIN GHAIRI HAULIN MINNIY WALA KUWATTA......._ *_~#HISNUL-MUSLIM.~_* *~__________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~__________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *0⃣7⃣* *K*okawa ta shiga yi da k'ofan,wanda da kyar ta samu ta bud'e...... K'ofan na gama bud'ewa idanuwanta sukayi arba da MA'U tsaye,idanunta sunyi jajur dasu kamar garwashi..... Kamar ance ta kalli k'afarta,ai kuwa nan ta hangi k'afar tayi busu²,dan k'ura da daud'a...... Duk k'ok'arinta na ganin ta kaucewa yin dariya abun ya faskara.... Nan ta fara tuntsirar dariya,kamar kwancen mahaukata....... MA'U dake tsaye tana jiran a bud'e mata k'ofa,taga ta tsaya tana mata dariya..... Tsaiwa tayi ta dafe saman gini,tana kallonta,sai dariya take,kamar sabuwar kamu....... Tsabar mugunta irinta KHUBRA har dafe gefen cikinta take,ita bata matsa daga kan hanya,ta bawa MA'U guri ta wuceba,ita kuma bata tsaida dariyan taba...... Kallonta MA'U taci gaba dayi,ganin abun nata ba na k'are bane,kuma ta rasa me KHUBRAN kewa wannan dariyan a tare da ita,abun ya soma bata haushi.... Ga haushin ta rufe mata k'ofa,sannan ta zo tana mata dariyar rainin wayo....... Hankad'ata tayi cikin soron,ta shigo tare da maida k'ofa ta rufe..... Wani gigitaccen mari MA'U ta aikawa KHUBRA da shi,wanda ta jishi,babu shiri kuwa ta had'iye dariyarta....... Gashin kanta ta dank'a ta jata zuwa cikin gidan,sai zage² take kamar y'ar maguzawa...... Babu zato bare tsammani MA'U ta shiga jibgar KHUBRA kamar ta samu jaka ko ince kayan wanki..... Tun tana dukanta KHUBRA na iya yin ihun neman ceto har ta koma muryanta ma bata iya fita saboda laushi da jikinta yayi..... Sai da tayi mata dukan sa'a,sannan ta yasar da ita a gurin ta shige d'aki,ba tare da ta furta ko 'A' ba,zuciyarta kamar zata fito waje saboda haushi..... KHUBRA dake yashe a k'asa babu,abunda ake iya ji na daga sautin muryanta,banda numfashinta dake fita da sauri²...... Ta jima kwance a gurin,wanda ta gagara koda motsin kirki...... *********** Tun tahowar MA'U da KHUBRA birni,hankalin ABBAN KHUBRA yak'i kwanciya..... Kullum cikin tambayar LADIYO yake yaushe MA'U zata dawo da ita..... Amsar dai guda d'aya ce kullum,dazaran lokacin da suka d'auka alk'awari yayi zata dawo da ita..... Shi kam kullum yana jinta ne,don kuwa ya fuskanci idon MA'U bud'e yake da son nera,tsoron sa d'aya kada su cutar masa da ita..... Abu sai dad'a gaba yake,LADIYO ta shiga tashin hankali ganin yadda malam en yake neman d'aga mata hankali,har bata so ya shigo ya tarar da ita zaune,yanzun zai dasa mata maganar y'ar tasa mai kama da aljanu..... Yau ma zaune take cikin y'ar rumfar karan dake bakin d'akin nata,wanda daga nan kana iya hango k'ofar shigowa gidan..... Zafi duk ya addabeta,daga ita sai d'aurin zani iya k'irjinta..... Malam buba ya kawo kai zai shigo cikin gidan,da sallama a bakinsa.... Ko amsawa bata yiba ta mik'e cikin hanzari zata bar gurin..... ''Dakata LADIYO,na fuskanci kwanan nan nema kike ki mayar dani wani sha ka tafi''..... ''Ko dai yau ki fad'amin inda y'ata take ko kuma aradu ina mai kai k'ararki gurin MAI GARI''....... Ido waje LADIYO ta juyo,nan ta shiga bashi hak'uri..... Saboda LADIYO irin matan nan ne masu d'an karen tsoro,ammafa akwai tsokana.... Idan akwai abunda LADIYO take tsoro a duniyarta kuwa baya wuce MAI GARI ko a ambaci mai bak'in kaya wato ('DAN SANDA)..... Har k'asa ta zube tana masa magiya,akan zata kira MA'U ta dawo da KHUBRA idan ma bata sametaba zata je da kanta ta dawo da ita har gida ba sai maganar ta jega HUKUMA ba..... Girgiza kai MALAM BUBA yayi,ya juya ya nufi d'akinsa ''Da dai yafi miki kwanciyar hankali''...... Yana fad'a ya k'arasa shigewa ciki..... LADIYO dake durk'ushe a inda MALAM BUBA ya barta ta d'ago tana dafe k'irji.... Ganin babu MALAM en a gurin tayi wuf ta fad'a d'aki.... Nan ta shiga raba ido kamar shege a rabon gado (yo dama me zai kawo shi tunda yasan bashi da ko allura)?..... Ita kad'ai ta shiga magana da kanta _''Ya zama dole nayi aron waya na kira MA'U ta dawo da wannan shegiyar yarinyar mai kamar aljana,tun kafin kashina ya bushe''....._ Ko gama tunanin batayi ba ta zara mayafinta ko riga babu ajikinta,tayi waje...... Bata zame ko inaba sai gidan k'awarta mai suna TABAWA..... ****** TABAWA irin matan nan ne y'an duniya,wad'anda suke da bud'ad'd'en ido..... Da shigarta ta tarar da TABAWA ta cokalo d'an kwalinta sai zabgawa mijinta rashin mutunci take.... Shi kuwa bawan Allah kansa a k'asa kamar wanda ke gaban uwarsa haka jikinsa sai b'ari yake..... Bata k'arasa shigowa ba ta tsaya daga bakin k'ofa,tana kallon wannan abun aljabi..... ''Dillah can banza kawai,zaka bani ko kuwa sai na cajeka? Katabbata idan har na laluba na tarar da kud'i a jikinka,wallahi yau kam babu kai babu cin abinci a gidan nan''..... Ta fad'a tana hak'ik'an cewa.... Rantsuwa ya shiga yi mata,sai kace d'a da uwa,amma hakan bai sa TABAWA ta yarda ba..... Rigarsa ta kama ta cukuikuyo shi,ta shiga lalube aljihunansa kaf,sai da ta tabbatar da abunda ya fad'a sannan ta kyaleshi tana fad'in ''Allah ya cece ka''..... ''Amma ba kyaleka nayi ba wallahi,zan ranta maka kud'in cefanen yau,kana samu kayi hanzarin biyana idan kuma ba hakaba,zaka had'u da tijarar da tafi wannan''...... Ita kam LADIYO na nan tsaye tamkar an dasa bishiya,ta lula cikin tunani,har bata san lokacin da mijin k'awar tata ya fita ba...... Dogon ajiyan zuciya tayi,kafin jiki a salub'e ta afko gidan ko sallama babu...... Binta kawai TABAWA tayi da ido A ranta kuma tana fad'in ko lafiya? *_~NIKO NACE OHO MUKU.........~_* *_~KEEP MOVING....~_*😍😍😍 *_REAL SMASHER_* 🤞🏻😘 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *Viawattpad@realsmasher01.* *©®2018* *25/mąrcɧ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~__________________________~* *ADDU'AR SANYA SABABBIN TUFAFI.* _ALLAHUMMA LAKAL HAMD ANTA KASAUTA NIHI AS'ALUKA KHAIRAHU WA-KHAIRA MAA SUNI'A LAHU,WA'A'UZU BIKA MIN SHARRIHI WA-SHARRI MAA SUNI'A LAHU..._ *~#HISNUL MUSLIM.~* *~__________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~__________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *0⃣8⃣* *T*ana nan kwance in da MA'U ta yasar da ita,kamar matacciya,idan ba wai mutum ya kula da yanda chest nata dake shibring ba,za a iya cewa ta jima da mutuwa.... ********** Cikin kwanciyar hankali MA'U tayi kwance kan gadonta,ko kad'an batayi nadamar abunda ta aikataba,bare ta duba taga halin da y'ar mutane ke ciki ba.... Idonta tar kan selling tana nazari kan wannan gidan aiki da ta samu.... Ita kam a nata ganin,da zaran ta samu wani aikin da yafi wannan maik'o zatayi watsi da wannan.... Ko dama ace ba a garin kuwa zatayi aiki ba,ita meye damuwarta,tunda ba ita ta haifeta ba..... Burinta bai wuce a kawo mata masu gidan rana...... ************ Wani uban tsaki TABAWA tayi lokacin da ta kalli LADIYO,da alama tunani take.... Da k'afa ta kai mata hauri... A firgice LADIYON ta d'ago tana k'ok'arin mai da kallabinta da yake shirin fad'owa.... Jajayen hak'oranta ta bud'e wanda babu abunda ke fitowa daga bakin nata banda wani irin azababben wari,ga su duk sun dafe saboda tsabagen daud'a..... Kallonta TABAWA tayi tana fad'in ''LADIYO ince dai ko lapia kike irin wannan dogon nazari haka?''..... ''Ke dai bari TABAWA ina cikin tashin hankali wollahi''.... Fuskanta da tsananin mamaki take kallon LADIYON da take koro mata jawabin abunda ya had'o ta da MALAM BUBA akan yarsa...... Dariyar mugunta TABAWA ta hau yi,tana tafe hannunta.... Sai da tayi mai isarta kafin ta saurara,tana k'arema LADIYO kallo,tana tab'e baki.... ''Uhmmmm!LADIYO kenan,ni ai a ganina ke kika so,da har kika tsaya MALAM BUBA yake zuba miki irin wannan rashin mutunci,da d'iban albarka haka Ni baki ganniba,washar da ni,tunda mu ba haihuwa za muyiba,ai gara muyi abunda muke so,kafin dare d'aya suzo mana da maganar k'arin aure''..... Baki bud'e LADIYO ke kallon TABAWA,da ta tak'ark'are tana koro mata datar...... ''Kinga yanzu ba zama ne ya kamacemu ba,abunda kawai za ayi,ki biyo sahuna,mu d'ora daga inda aka tsaya.... Har zamu tsaya ne muna kallonsu,mu tashi a tutar babu,shi kenan munyi ba wan ba k'anin?''..... Karatun na d'an kama...... "Ina kuma zamu nufa yanzun?" LADIYO tayi tambayar..... "Kinga yanzu ba lokacin tsaiwa dogon jawabi bane,idan kina da buk'atar mafita kawai ki taso,bana son dogon sharhi"..... Jiki na b'ari ta mik'e tabi TABAWA a baya,kamar RAK'UMI DA AKALA...... ************ Rashin madafa shi yasa KHUBRA dake kwance,lallab'awa da jan ciki,ta d'ebi ruwa a buta...... Da yake lokacin zafine,ruwan da zafinsa,rana ta gama gasashi.... Haka ta lallab'a ta shige,wanka tayi ta d'aura alwala ko za taji dama².... Da kyar ta iya mik'ewa tana bin bangon toilet en,ta fito daga ciki,jikinta duk ya mata nauyi.... Haka ta ci gaba da takowa tana d'aga k'afa da kyar,har ta samu ta fito...... 'Daki ta shiga da niyyan ta samu ta lallab'a tayi sallah,dan kuwa lokacin har an idar da sallar maghreb...... Ko da ta shiga d'aki da sunan za tayi sallaah...... 'Dagowa MA'U tayi,tana K'are mata kallo..... Cikin tsawa ta hau fad'an da tun d'azun batayiba..... ************ Can cikin wani surk'uk'in hanya suka shiga bi jikin LADIYO sai kyarma yake saboda tsoron hanyan da ko a mafarki bata tab'a tsintar kanta a cikiba.... Bin bayan TABAWA kad'ai take,wacce ita kam ko d'ar bata jin tsoron komai,haka take watsa k'afafuwanta cikin jejin..... Haka har suka tsinci kansu gaban wata y'ar bukka dake saman wani sand dune hill.... TABAWA da yake tasan kan hanyar yanda ake hawa,haka ta shiga raba k'afafuwanta,har ta ida hawa..... LADIYO kam ta kasa hawa,sai ta hau sai ta dawo k'asa,jikinta duk ta kurjeshi garin k'ok'arin hawa.... Daga saman dutsen TABAWA ta hango LADIYO yanda take ta faman kaiwa da komawa dariya ta tuntsire da shi,nan ta shiga kokawar komawa k'asa..... Kokawa suka shiga yi na hawa,in da TABAWA ta rik'e hannun LADIYO kamar wasu k'ananan yara,tana koya mata yanda zata hau,har dai sukayi nasarar hawa saman dutsen..... Guri suka samu suka zauna kan wasu fatu dake shimfid'e uwa tabarma,suna jiran zuwan mai gurin..... _KUYI HAK'URI DA WANNAN FAN'S..._ *_REAL SMASHER_* 🤞🏻😘 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *Viawattpad@realsmasher01.* *©®2018* *27/mąrcɧ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~__________________________~* *ADDU'AH IDAN KAGA WANI DA SABON KAYA.* _TUBLIY WAYUKHLIFULLAHU TA'ALA...._ _ILBIS JADIDAN,WA'ISH HAMIDAN,WA-MUT SHAHIDAN._ *_~#HISNUL MUSLIM.~_* *~__________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~__________________________~* _Aradu kuna bani dariya fan's en *Y'AR GARUWA* ,labarin nan gaba d'aya yanzun aka fara har hanzun ba ayi komaiba,kuci gaba da biyoni dan jin yadda za ta kasance.... *LUV U OLL.*_ 💔 *~__________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *0⃣9⃣* *B*ayyanarsa kawai LADIYO ta gani wanda ba k'aramin tsorone ya cika mata zuciya ba.... Jikinta sai kyarma yake,duk ta firgita,sai neman b'oyewa da take a bayan TABAWA..... Dariyar da ya kece da ita,wadda ta haddasawa d'an k'aramin forest en amsawa,mai kama da kukan jaki.... Ita ta sake rud'a LADIYO wadda a sanadin hakan har fitsari ta soma,ta mak'alk'ale TABAWA..... Wata razananniyar tsawa ya mata yana fad'in ''Shiga hankalinki la'ananniya,b'atacciya,duk wanda yazo nan ya tabbata wakilin shaid'an,bama wa muminai aiki.... Idan kin san da sofanen imani a tare da ke maza ki b'ace anan tun kafin yaran shaid'anu su sauke fushinsu akanku''..... Ya k'arashe maganar yana zare jaajayen idanunsa,masu kama da garwashi...... ''A tafiyarmu babu tsoro,bamu san mene shiba bare muyi shi,idan har kin kiyaye wad'annan sharud'a,muna maraba dake yar jakar uba''..... Ya sake kecewa da wata dariyar da ta fi ta farko.... Ita kam LADIYO yanda yake magana da dariyarsa shi yafi komai tayar mata da hankali..... Harara TABAWA ta aika mata wadda tasa ta shiga hankalinta,ta zauna sosai,amma da zaka ce mata kyattttttt to kuwa zaka nemeta ka rasa.... Kafin su kaiga yin magana ya tare su yana fad'in ''Bana buk'atar kuce wani abu,nasan abunda ke tafe daku''..... KEEE ya nuna LADIYO,kafin ya d'ora daga in da ya tsaya.... ''Akan mijinki ne da kuma y'ar kishiyarki wacce mahaifiyarta ta rasu''..... ''Me kike so a yi wa mijin naki? Kina so a kasheshi ne,ko kuwa a rabashi da y'arsa kamar yanda ya rabu da iyayensa, kar ya sake tambayarki in da take,ko kuwa kina so ya koma jin tsoronki tamkar ke kika haife shi?''... Gyad'a kai tayi cikin farin cikin samun mafita,sannan ta shiga yi masa bayanin abunda take so ayi musu akan MALAM BUBA..... Haka bokan nasu ya juya yana mai kecewa da dariya ya shige bukkar tasa...... Wasu uban layu ya fiddo ya mik'a mata... Kinga wannan ya nuna mata wata k'arama daga ciki,zaki sata a cikin matashin kanki da kike bacci (pillow).... Wad'annan kuma ki samu dai² bakin k'ofar d'akinsa ki hak'a rami ki binne su,idan kikayi haka kuma aikinki ya kammala,sai ki jira kiga mai zai faru''...... Ku tashi ku bani guri....... LADIYO da shishshigi sai cewa tayi ''MALAM mene ne kud'in aikin nawa?''..... Tsawa ya watsa mata yana fad'in ''Kaji y'ar jakar uba,mu nan ba a tab'a biyanmu idan mukayi aiki sai bayan aikinmu ya kammala..... Maza ku bar nan,kada ku sake ku waiwayo''..... Cikin sauri ko wacce ta suri takalminta suka kamo hanyar barin jejin,ko da wasa babu wacce ta juya,har suka fito daga ciki..... ********** A fusace MA'U ta mik'e tana shirin dank'o KHUBRA da tayi tsaye.... Ba shiri tayi waje har tana neman fad'uwa du da dama jikintan ba wani k'wari ne da shiba..... ''Da kin tsaya ai y'ar jakar uba,yau da na nuna miki k'aryarki,dan yau na lahira sai ya fiki jin dad'i''..... Ta fad'a tana huci,sai jijjiga jiki take,uwa wacce take shirin fad'a da sa'anta.... Komawa tsakar gidan tayi,nan ta shimfid'a d'an kwalinta,tayi sallah,ta ci gaba da jiran gawon shanu..... Sai da ta raba dare a zaune a gurin ba tare da ta motsa ba.... Lokacin da ta tabbatar da LADIYO tayi nisa a cikin baccinta,ta mik'e ta lallab'a.... Gurin kayanta ta dosa d'an ragowar k'uli²n da ABBANTA ya bata shi ta d'auko ta ci,ta sake d'aurewa ta mayar... Ta d'ebi ruwa ta sha,tayi godiya ga mahaliccinta.... Har ta gama abunda za tayi a d'akin MA'U bata san ta shiga ba..... Sake komawa ta sake yi ta d'auko zani a cikin kayanta ta fito tare da jaa mata k'ofan.... A inda tayi sallah ta shimfid'a,hijab en jikinta kuma ta cire shi ta lullub'e jikinta.... Takurewa tayi guri d'aya saboda rashin girman hijab en ba zai kai mata ta rufe jikinta gaba d'ayaba..... A wannan daren sai dai da yake an ce bacci b'arawo ne,amma da KHUBRA zata iya cewa ba zata iya bacciba... Duk da baccin nata ya kasance rabi² ne.... Sai bayan da tayi sallan Asubah sannan wani nannauyan bacci yayi gaba da ita....... ************ Shigowar MALAM BUBA gida yana ta kwad'a sallama,yaji shiru ba'a amsa ba.... Nan ya shiga kiran LADIYO,jin shirun yayi yawa,ya shiga nemanta lungu da sak'o na gidan,amma ko mai kama da ita bai ganiba bare kuma itan.... Girgiza kai yayi ransa a b'ace yake fad'in ''Duk inda kikaje zaki dawo ki tarar da ni,kuma xa kiyi bayani,wannan iskancin na gaji da shi''..... Yana gama bambamin fad'an nasa yayi waje...... *********** Kamar yadda ya musu bayani,direct gidan LADIYO suka nufa.... Gidan babu kowa,kasancewarsa haka kuwa da shigowarsu,suka hau dube²,bayan sun tabbatar babu mutum ciki,suka hau aiwatar da nufinsu...... Sai da TABAWA ta tabbatar sun gama aikata komai kamar yadda aka fad'a musu tukun,ta sake d'orata akan hanyar b'ata,wacce su a ganinsu ita ce dai²...... Sannan tayiwa LADIYO sallama,ta nufi hanyar nata gidan,babu fargabar tayi dare bata dawoba,za ta tarar da fad'a...... ********* Sai da gari ya gama wayewa sannan MA'U ta fito daga d'aki.... Kamar kullum cikin al'adunta,tana hamma had'e da mik'a..... Mutum ta gani kwance,sai alokacin ta tuna abunda ya faru...... Batayi magana ba ta wuce bakin randa,sai da ta cika bokiti da ruwa,ta d'auko shi da k'yaar.... A dai² kan KHUBRA ta d'aga shi ta juye mata shi a kanta.... A firgice KHUBRA ta mik'e tana dube²......... *_~#TEAM KHUBRA...~_* *_REAL SMASHER._* 🤞🏻😘 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *Viawattpad@realsmasher01.* *©®2018* *28/mąrcɧ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~__________________________~* *ADDU'A YAYIN CIRE TUFAFI.* _BISMILLAH!!_ *ADDU'A IDAN ZA A FARA ALWALA.* _BISMILLAH!!!_ *_~#HISNUL-MUSLIM.~_* *~_________________________~* _Sisinah ina miki fatan alkhairi arayuwa,ubangiji ta tashi kafad'unki,ina missing enki sosai na rashin kasancewa tare da juna.._ _Wish u a very quick and speed recovery *MY HUBBEEY* ,I so much heart u cweety.._💔💔💔 *~__________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~__________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *1⃣0⃣* *T*saye akanta taga MA'U da k'aton bocket,tana ta faman aiko mata da uwar harara.... Mik'ewa tayi tana kama kayan tana matsewa... Sunkuyawa tayi ta kamo zanin da ta shimfid'a... Ko kafin ta kai ga d'aukowa MA'U dake tsaye bayanta ta d'irka mata hannunta mai kamar na maza a bayanta.... Lank'washewa tayi a gurin saboda azabar dukan da ya shigeta,ko bata fad'a ba.... Kuka ne ya kufce mata,ta shiga rerawa babu saurarawa... Kamar mutuniyar arziki haka MA'U ta juya,a bakin randan ta ajiye bocket en ta sake dawowa ta wuce KHUBRA dake faman kuka uwa ranta zai fita... Sai da ta kalleta kafin ta wuce cikin d'akin,ta d'an jima aciki sannan ta fito... Hannunta d'aya a goye a bayanta,ta nufo inda KHUBRA take sunkuye ta saka fuskanta a tsakanin laps nata... KHUBRA da bata san meke faruwa ba bare tasan abunda zai faru nan gaba,sai jin duka tayi ta ko ina yana ratsa jikinta.... K'ok'arin karewa ta shiga yi,amma hakan ya gagara... Gaba d'aya MA'U ta hanata motsi,ta kama ta nad'eta acikin hijab enta.... K'ok'arin guduwa ta shiga yi,ga MA'U bata daina dukanta ba,ganin azaban yayi mata yawa yasa ta dage ta ingije MA'U ai kuwa nan sai ga MA'U a k'asa timmm.... Da gudu ta nufi hanyan fita daga gidan.... ''Kada ki kuskura ki fita daga gidan nan,dan wallahi na lahira sai yafi ki jin dad'i yau,yarinya zaki gane ni kika tura na fad'i''... Tana daga kwance a inda KHUBRA ta tura ta take koro bayani... Da k'yar ta mik'e daga gurin tana d'ingishi,haka ta koma d'aki tana duba jikinta... Hannayenta ta k'urje su,ga d'an yatsanta na k'afa da yake mata rad'ad'i.... MENTHOLATOM ta hau gogawa gurin... Azabar da yake mata ce ta sata bari babu shiri... Haka ta kafawa d'an yatsan nata ido,ganin ya soma kumbura ta tabbatar ta samu targad'e... Dafe kai tayi tana jin rad'ad'in da yatsan ke mata har tsakiyar kanta... Lallai wannan yarinya koi ja'ira,amma babu komai ta ciji lips enta, ''Zanyi maganinki'' Ta furta ciki²..... ************* Haka ta shige d'aki ko tunanin sallah batayi ba,tana shiga kuwa ta turo k'ofar d'akin nata... Kwanciyarta tayi take kuwa bacci yayi awon gaba da ita.... K'arfe 9:15pm MALAM BUBA ya nufo gidan nasa,da tunanin ko LADIYO ta ga dama ta dawo? Tun da ya tunkaro gidan gabansa ke faman fad'uwa... Bai kawo komai a ransa ba,haka ya shigo gidan,k'ofar dake jingine ya d'aga ya karata a saitin k'ofan... Juyawa yayi ya shiga da sallamarsa... Da yake yasan ma koda tana nan ba amsawa za tayi ba,hakan ya sashi wucewa d'akinsa..... Jiri ne ya fara neman kada shi,da sauri ya dafa wall en d'akin,ya daddafa ya shiga ciki,tun da ya shiga d'akin bai sake sanin inda kansa yake ba...... *********** Lek'owa tayi tana daga soron,jin shiru da tayi,shi ya bata tabbacin bata gurin... Da sand'a ta shigo ta lallab'a ta kwashe kayanta daga gurin.... Kan wall en toilet en gidan ta kai ta shanya,ta dawo ta nemi guri ta zauna tana jiran gawon shanu,nan ta sake lulawa duniyar tunani... 'Daga labule taga anyi,ai kuwa karaf akan idonta... zaraf tayi ta mik'e tsaye,tana rab'ewa gefe.... Harara MA'U ta aika mata,ta wuce ta shiga toilet,kamar ko wane lokaci,kafin cikar mintuna biyar har ta fito.... Kallon KHUBRA tayi kafin cikin wata irin murya ta hau fad'in ''Uban meye kike jira a nan? Ki zo ki wuce ki samo ruwa sannan ki tabbata kin sharemin gidan nan''... Sum² ta zo ta wuce,haka ta d'auki k'aton bocket en da MA'U ta ajiye,ta jaa silifanta tayi waje... Lokacin da ta fita rasa ina zata nufa tayi,coz tun da tazo yau ne rana ta farko da ta fara fitowa... Ta jima tsaye tana tunanin in da ya kamata ta nufa.... Tambaya ta yanke shawaran tayi,amma wa zata tambaya? unguwan shiru,babu kuma masu wucewa.... Haka tayi ta tsaiwa a gurin.... Gajiya tayi da tsaiwan,zuwa wani lokaci har ra fara gumi,haka kan dole tabi ra'ayin zuciyanta.. Gidan dake gefensu ta nufa,sallama tayi ta shiga... Babu kowa a tsakar gidan,sai wata mata da ta gani tana fitowa daga d'aki... Da d'an murmushi akan fuskanta ta amsa mata,tana fad'in ''Maraba,k'araso daga ciki''.. Murmushin itama KHUBRAN tayi tana fad'in ''Laa da kin barni ma daga nan''... Gaidata KHUBRA tayi,kafin ta shiga tambayanta inda zata sami ruwa.... ''Laaa kinga ai ba nisa ma,kina fita akwai gida da yake kallon nan,suna da rijiya''-.... Godiya tayiwa matar ta kama hanya ta fice,matar na binta da kallo.... Haka ta shiga gidan,suka gaisa da matar mai kirki,sai jan KHUBRA take da fira,ita kam ta kasa sakin jiki da ita,haka taita kaiwa da kawowa,har ta kammala d'iban ruwan..... Bayan ta kammala haka ta duk'ufa kan shara,zuwa wanke²... Lokacin da ta gama tana murna za ta huta,har ta nemi guri ta zauna,MA'U ta lek'o tana fad'in ''To hakima ba zama za kiyi ba,maza duba wancan d'akin akwai kwanuka maza ki tattarosu ki wanke su,idan kin gama kimin magana.... Haka ta shiga tattaro kayan wasuma har sun fara fungi,wani kuwa cikinsa yayi bak'i kamar an shafa kwalta... da k'yar ta gama wankewa,ko da ta gama haka ta kwashi k'afafunta ta je k'ofar d'akin ''Na gama'' abunda ta iya fad'a kenan... ''To jirani'' MA'U dake d'aki ta fad'a.... Fitowa tayi da uban kaya a hannunta,haka ta watso mata su,ta sake komawa ta d'ebo wasu... ''Ga shinan maza ki tabbatar kin wanke su sun fita tas,dan idanma basu fitaba,zaki sake ne''... Juyawa tayi tana k'arewa kayan kallo,gasu da uban yawa,ga kuma daud'a,wanda ko kayan d'an goye ba zai nuna musu daud'aba.... Har ta kai bakin k'ofa KHUBRA ta furta ''Sabulun wankin''.... Shigewarta tayi,sai da ta gama b'ata lokaci,sannan ta cillo mata... Haka tayita gurzarsu,babu iyaka,har dai ta samu ta kammala,lokacin ana kiran sallan ISHAA..... Ranar gaba d'aya KHUBRA haka ta yini aiki daga wannan sai wancan... Haka ta tashi jikinta sai kyarma yake,ga ciwo da yake mata,ga tsananin yunwa,ga uban ciwo da kanta yake tamkar zai rabe... Tashi tayi da k'yar ta tattara kayan da tayi amfani dasu,ta shiga d'akin shirgin nan ta gyara shi,duk da tana cikin wannan halin haka ta share shi... Ruwa ta d'iba ta shiga ta wanke jikinta,sannan ta d'auro alwala,ta fara jera sallolin da ake binta bashi,dan kuwa MA'U hanata tayi ta motsa ko nan da can... Tana yi tana ZUBAR HAWAYE,tana rok'on Allah gafara da kuma neman d'auki daga gare shi..... Ta jima acikin sujudah tana rok'on Allah,kafin ta d'ago tayi tahiya,ta sallame.... Da k'yar ta iya motsawa daga gurin,ta lallab'a ta fito daga d'akin... 'Dakin MA'U ta shiga sai tare kanta take da hannu wanda ke mata barazanar fashewa... ''Dan Allah BABA ki taimakamin da abunda zan ci,wallahi ina tsananin jin yunwa,kuma kaina ciwo yakemun'' Ta fad'a kamar zata fad'i.... ''Ke dallah dakata,karki fad'o kaina,dan kina jin yunwa shi ne me? Malalaciyar kawai,d'an wannan aikin da kikayi kinzo kina min raki''..... Haka MA'U ta koroto ba tare da ta tausaya mataba... Kuka ta fashe da ta nemi guri abakin d'akin ta shiga rerawa... Ashar en da MA'U ta k'unduma ne ya sata tsagaitawa... Kamar daga sama ta ga MA'U da jakar kayanta a hannu,cillo mata tayi tana fad'in ''Idan zaki iya tafiya bismillah,abincine banga dama ba,kina iya ki nema da k'arfinki sai ki ci...... *_~#TEAM KHUBRA.~_* *_REAL SMASHER._* 🤞🏻😘 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *30/mąrcɧ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~__________________________~* *ADDU'AR SHIGA BAN'DAKI.* _BIMILLAHI!!! ALLAHUMMA INNIY A'UZHUBIKA MINAL-KHUBSI WAL-KABA'ISI.._ *ADDU'AR FITOWA DAGA BAN'DAKI.* _GHUFRANAKA...._ *_~#HISNUL-MUSLIM.~_* *~_________________________~* _The hole page goes to masoyana kuma masoya novels en *RAYUWAR WANI* da *Y'AR GARUWA* ,iya wuya ina k'aunarku nima kamar yadda kuke k'aunata Allah ya barmin ku aduk in da kuke..._ *_~#REALLY HEART U GUYS..~_* 💔💔💔 *~_________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~__________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *1⃣1⃣* *T*ana gama fad'an haka ta juya ta shige d'aki,ba tare da damuwan komai a rantaba... Sai da ta gama cin kukanta sannan ta tashi,ta tattare kayanta da suka zube,ta mai da su ciki.. 'Dakin da ta gama gyarawa ta shiga ta sa kayanta daga gefe... Nan ta takure guri guda tana mai had'a kai da k'afa,tana tunanin wannan rayuwar da ta tsinci kanta a ciki... Cizon sauro shi yafi takurata,a d'akin haka suke kawo mata farmaki,ga zafi.... Zaman dirshan ta yi bacci ya gagareta,banda koran sauraye babu abunda take,wanda shima da k'yar take iya d'aga hannunta,daga k'arshe ma kasawa tayi,haka ta bar su tanaji tana gani,suke kawo mata farmaki... Tana daga zaune ta jingina kanta a wall en d'akin,abun tausayi ga jikinta sai faman ciwo yake,ta rasa inda zata sa kanta,saboda azaba kanta kamar zai fad'o haka take jinsa,yanda take ji yasa ta fara cire tsammani da rayuwar duniyar... Bakinta banda motsi babu abunda yake,da kallo kasan ba abunda take da ya wuce addu'a... Idanunta a rufe haka hawaye ke layi ta gefen face enta,kukan ya gagareta..... Da k'yar ta tashi lokacin da taji kiran sallah da asuba tana bin bango haka tayi alwala,ta sake komawa d'akin... A daddafe tayi sallah daga zaune,ko addu'ah bata samu daman yi ba,wani wahalallen bacci yayi gaba da ita... ********** Ba shi ya farka ba sai da gari ya gama yin haske,rana harta faso a garin... Cikin wani irin yanayi na mutuwar jiki haka ya mik'e ya fita,yayo alwala ya dawo,a d'aki yayi sallah ya idar,haka ya zauna yana tunani amma ya rasa mai zai tuna... A ganinsa akwai wani abu mai muhimmanci da yake son tunawa da shi,amma ya kasa tuna wannan abun... Badan ya soba haka ya k'yale kansa,yana mai mik'ewa yayi hanyar fita daga gidan.... *********** Har gari ya gama haske rana ta gama haske garin,MA'U bata farka ba,haka itama KHUBRA,Bacci take a wahale... Sai wajen k'arfe 12:30pm KHUBRA ta farka... Idanunta take bud'ewa a hankali,duk sun kumbure saboda bata wani samu isashshen bacciba... Sai da ta gama bud'esu tar,sannan ta mik'e ta zauna,sai da ta zauna ta huta... Jikinta ba kamar da dare ba,yanzun har tana iya mik'ewa sosai,kantan kuma ta d'anji sauk'insa... Kayanta ta tattare tana had'asu guri d'aya... Tunawa tayi da abunda MA'U ta mata jiya kan dole ta mik'e ko dan kar a maimaita irin jiyan,ta d'auka tsintsiya tayi tsakar gida... Tsaf ta share gidan ta,d'ebi ruwa tayi wanka,haka ta zauna a tsakar gidan,rana sai sake matsowa inda take..... MA'U ce ta fito daga d'aki tana mik'a,ta nufi band'aki kamar wacce ake tunkud'awa,haka ta fad'a band'akin kamar an cillata,ko addu'ah babu... Kamar sakkowar ruwan sama haka ta saki fitsarin da shigarta... Tab'e baki KHUBRA tayi tana daga wajen,fuskarta duk maik'o... A ranta take fad'in ''Wama ya sani ko ta fara a kwance ne?''... *********** Tun fitowar ABBAN KHUBRA daga gida bai koma ba,haka ya yaci gaba da rayuwarsa a waje.... LADIYO an shanya baki sai bacci ake,ba ita ta tashiba sai azhur,ba don ta so tashin ba,sai dan cikinta dake ihun yunwa,fun da ta San babu wanda zai bata tana kwance... Ba tare da tunanin gaida mahaliccinta ba ta shiga neman abunda za taci, rashin komai a gidan, yasata bazama neman MALAM BUBA haka take cilla fasassun k'afafuwanta... Kitchen ta sake lek'awa neman duniya tayi aciki babu komai cikinsa sai busashshen k'anzon tuwo ta tsinto... Haka bbau komai ciki bare mahad'i tayi ta garzarsa kamar akuya har ta cinye,sannan ta fito daga ita sai d'aurin zani iya k'irjinta.... Sai bayan ta samu nutsuwa ta zo mata tukun,wani tsoro ya sakko mata,tunanin abunda ya faru jiya ya dawo mata,nan ta tafi duniyar tunani... ''Shin yanzun idan duka wannan abun ya tashi a tutar babu fa suyi yaya ?'' Tunaninta ya tsaya kan da me zata biya kud'in aikin idan har aikin yayi,nan take wani mummunan tsoro ya sake cika zuciyar LADIYO.... ********** Sai da ta gama yauk'inta a cikin d'aki sannan ta fito tana jan k'afa,coz har yanzun ita kad'ai ta san me take ji saboda azabar da yake mata,k'afar duk ta dad'a hawa tamkar kwab'in bread...... A kan KHUBRA ta ja ta tsaya, #50 ta cillo mata cikin tak'ama tace ''Idan zaki iya ki je ki nemo garin kwaki,a shago''.... Ko gama fad'a KHUBRA bata jira tayi ba tayi waje,da hope en ta take tafiya,tana neman shagon da zata siyo garin.... Tayi tafiya mai nisa sosai sannan da tambaya ta samu ta siyo.. Kamar kowane lokaci haka take tafiya,kanta a k'asa,tafiya take har ta kusa da gida... Kamar daga sama taga an tsaya gabanta.. Da sauri ta d'ago tana kallonsa kamar zai fad'o kanta saboda yanda yake layi.... Hannunsa da wani cukuikuyayyen tsumma,sai dannashi yake a baki... Idanunsa sun gama rinewa uwa an watsa musu colour.... Wani dariya yayi yana mik'a hannu da shirin damk'ota,yana fad'in ''Y'an mata zo mana''... Da sauri KHUBRA ta durk'she a gurin jikinta banda rawa babu abunda yake.... Sunkuyawanta shi ya bashi damar dank'an iska,ya sake mik'o hannu zai sake kamota.... Ai KHUBRA kam kan kace mene wannan ta k'arawa k'afafunta wuta,gudu take tamkar taga naman jeji.... Biyota ya shiga yi,yana maganar da ita kam bata san me yake fad'aba.... Gudu take tamkar k'afanta zata cire kan gudu,tana zuwa k'ofan shiga gidan ta daketa da k'arfi tayi ciki,ko tsayawa ta rufe bataiba... Tai ciki a guje sai d'akin MA'U wanda tana kwance tana jiran dawowan KHUBRA ta ji an fad'o d'akin,kamar an tsikareta ta mik'e tana dafe chest enta.... Cikin tsoro kamar ita tayi gudun ta hau haki tana fad'in ''Me ya faru?''.... KHUBRA ta kasa magana sai k'ofa da take nunawa MA'U.... Ganin tana neman raina mata hankali shiya sata doka mata wata uwar tsawa,data sa jikinta sake ci gaba da rawa kamar an jona mata shocking.... Zuwa wani lokaci jikinta ya jik'e da gumi kamar an watsa mata ruwa.... Magana MA'U ta jiyo daga zaure,hakan ya sata lek'owa ta ga ko waye..... Mutum ta gani sai layi yake,tana lek'awa ta dawo tana fad'in ''Caarrr uba dama wai abunda kikema gudu kenan,shegiya y'ar bak'in ciki,kin zo kin wuce ko kuwa sai na b'ab'b'laki............. *_~#Ido na zare ina fad'in ''ina za ta,ba dai gurin wancan d'an magarunba.....~_* ____________________________ _MASOYA *RAYUWAR WANI* INA BAKU HAK'URI NA RASHIN TYPING DA BANYI BA A YAU,COZ KWANA BIYU INA JINA SAI AHANKALI,BANA JIN DA'DI SOSAI,INA FATAN ZAKUYIMIN UZURI.._ _____________________________ *_~#TEAM KHUBRA.~_* *_REAL SMASHER_* 🤞🏻😘 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *1/ąpril,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ *ɛɖıɬɛɖ ცყ* _HAFSAT M.U {rɛąl ɧą℘cყ}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~__________________________~* *ADDU'AH IDAN ZA A FARA ALWALA* _BISMILLAH!!!_ *ADDU'AH IDAN AN GAMA ALWALA* _ASH-HADU AN-LAA ILAH ILLAH,WAHDAHU LAA SHARIKALAHU,WA-ASHHADU ANNA MUHAMMADIN ABDUHU WARASULUH..._ _ALLAHUMMA JA'ALNIY MINAT-TAWWABIYNA,WAJA'ALNIY MINAL MUTA'DAHHIRIYNA..._ _SUBHANAKALLAHUMMA WABI HAMDIKA ASHHADU ANLAA ILAHA ILLA ANTA ASTAGHFIRUKA WA-ATUBU ILAIK..._ *_~#HISNUL-MUSLIM~_* *~__________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~__________________________~* _Y'an uwa muna barar addu'ah daga gareku sis ena babu lapia,jikinta ya sake tashi da fatan Allah ya tashi kafad'unta.._ _Wish u a very quick and speed recovery MY HUBBEEY_ *~_________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *1⃣2⃣* "Dan Allah BABA kiyi hak'uri wallahi d'an shaye² ne,sai neman fad'omin yake a ka d'azunma"... "Ai wallahi yau ko nemanki zaiyi sai kin fita idan kuma ba haka ba na rantse sai jikinki ya fad'a miki".... Tsaiwa taci gaba dayi jikinta sai rawa yake... Ganin tana neman raina mata hankali yasa MA'U ta fice ta nufi d'akin shirginta... Fitowa KHUBRAN tayi daga d'akin dan tun da taga ta fita tasan ba zasu kwashe ta dad'iba.. Karo sukaci da MA'U ta d'auko tab'arya,a guje tayi waje tana rafka ihuu... Taimakon da Allah yayiwa KHUBRA lokacin da MA'U ta lek'a bayan ta dawo shi kuma ya juya ya fice yana faman tangad'i,ya nemi hanya yaci gaba gara rayuwarsa... Tana fita ta tarar babu kowa,wannan shi ya bata sauk'i da ta fita bata ganshi ba tayiwa Allah godiya... Ta d'an jima a tsaye a waje kafin ta juyo ta dawo da k'arfin gwuiwarta... Wani malalacin kallo MA'U tayi mata wanda yasa ta sha jinin jikinta... Kanta a k'asa ta gagara d'agowa... ''Munafuka da ana kije kina k'i yanzun daga wane gidan uwar kike?'' Ko tari batayi ba bare ta amsata,hakan yasa ta mik'o mata hannu tana fad'in ''Bani abunda kika samo''... Idonta a waje take kallon MA'U ''Wallahi BABA banma ganshiba da na fita ''.... ''Gidan wace uwar kika zauna da kika tarar bayanan?''.... ''Sai ki wuce ki d'auka wancan abun ki ci''... Sum² ta wuce ta d'auka tana shigewa d'akin shirgin nata.... Jik'awa tayi haka ta k'asumawa cikinta ko isashshen sugar babu a ciki... Tun zuwanta garin wannan shi ne karo na farko da wani abu ya shiga cikin hanjinta,baya ga k'uli² da tayi ta k'amusa.... Tsaf ta share wanda ta jik'a, ita kuwa gogar spaghetti ta d'auko ta silala jellop akan idon KHUBRA sai k'amshi take ta sa gaba ta ci iya cinta... Tana gamawa ko mintuna 10 bata k'araba a gidan tak'arawa k'afafunta wuta.... Sai KHUBRA dake faman gadin gidan ita d'aya.... Tana nan zaune tana fama da sana'ar tata,nan wani daddad'an bacci yayi gaba da ita... ************** ''Please Ki tsaya ki saurare ni my princess,nasan dai dawowan da nayi kike mamaki,ya akayi na dawo,fushi da ke bazai kaimuba.. Wannan kukan kuma bana son ganinki kina min asarar wad'annan precious tears en''... 'Dan murmushi sukama juna... Kafin yaja hannunta yana fad'in ''Muje muyi fira toh'' Ya shiga janta zuwa wani k'ayataccen garden.... Gaba d'aya gurin ya k'awatu da wasu irin green en grasses,baya ga dogayen bishiyu masu tsananin kyau,gefe guda kuma k'orama ce take gudu ta ratsa ta cikin lambun.... Can daga gefe wasu fararen tattabaru ne suke shawagi daga sama zuwa k'asa suna wasansu,sai kukan tsuntaaye da ya dad'a k'awata shirun gurin... Akan grasses en suka zauna,basu kai ga saman fararen kujerun dake zagaye da gurin ba.... Kansa ya d'ora akan cinyanta,suna firansu mai ban sha'awa... Sai wasa take da bak'in suman kansa.. Idanunsa a lumshe kamar mai bacci,zuwa can ya mirgina yana kallon fuskanta... Ganin kallon ba na k'are bane ta sunkuya dai² fuskansa ta hura masa iska,wanda ya sashi wani ajiyan zuciya... A hankali ya shiga bud'e eyes ensa da suke brown colour tsakiyansu da wani haske tamkar na mage... Janyota yayi yana mik'ewa zaune.. Fuskanta ya tallafe da hannu,ya dad'a matso da ita yanda suna jin fitar numfashin juna... Bai jira komaiba ya had'e bakinsu guri d'aya sun jima haka,kafin wasan nasu ya canja salo.... Sunyi nisa acikin wata duniyar,wanda gaba d'aya KHUBRA a tsorace take da al'amuransa... Turashi ta shiga yi amma ta kasa breaking abunda ke tsakaninsu... Saboda rik'on da yayi mata ba na wasa bane.. Kuka ta fasa masa,wanda ya sashi cikata babu shiri,yana kallon cikin idonta.. ''Haba wifey me kike nufi kuma,nifa naki ne,kuma ke tawa ce.. Yin haka dai² yake da nuna rashin kulawarki a gareni''.. Ita kam kukanta take babu ji... Tun yana rarrashinta har abun ya soma bashi haushi... Mik'ewa yayi a fusace yana shirin barin gurin... Da sauri ta rik'o hannunsa tana girgiza masa kai... Fisgewa yayi yana ci gaba da jaa baya.. Cikin wani irin murya ya soma fad'in ''Idan har na tafi daga gareki a yau ba zan sake ko da waiwayowaba... Wancan lokacin na juyo zuwa gareki,amma wannan karon kada kiyi tsammanin sake ganina''.. ''Dan Allah kayi hak'uri ka saurareni''.... Ci gaba yayi da tafiya ba tare da ya saurareta ba bare ya ji me zata fad'a.... ************ Cikin wani irin firgici ta farka daga nannauyan baccin da yayi gaba da ita... Dafe saitin zuciyanta tayi saboda wani irin matsanancin bugu da yake mata... Tsoro duk ya gama bayyana a tare da ita.... Ta kasa fuskantar komai da ya danganci mafarkin nata,hatta kuwa da fuskansa da ta gani,ta kasa tunawa... Tashi tayi da niyyan yin alwala,sai dai abunda ta gani ya sata fara kuka kamar wadda ake fitarma da rai.... *********** Duk son duniya irinta LADIYO yau itace taci k'anzo abunda bata tab'a tsammaniba ko da a mafarki... Gidan ta shiga bincikewa ko zata samu d'an wani abun da zata ci da rana.. Tunda ta fuskanci MALAM BUBA baya gidan yau kam,kuma zaiyi wuya ta ganshi.... Kaf ta gama bincika ko ina amma ko k'wayar shinkafa bata samoba... Haka ta dawo ta zauna a rumfa,kamar wata mutuniyar Allah.... *********** 'Bangaren MA'U kuwa yini tayi neman abun duniya,sai sake cigiyan gidajen aiki take dan ita har ga Allah wancan ya mata arha da yawa... Shi yasa ta yanke shawaran sake neman wani ko za a dace,amma ina haka ta yini tana yawo a gari.... *********** Duk da bawai yau ta fara ganin hakan a tare da ita ba,haka ta zauna tana kukan... Coz ta san halin MA'U za ta iya cewa yawon iskanci taje.... Kukan da tagani ba shi ne mafita a gareta ba yasa ta bawa zuciyanta hak'uri,ta mik'e.... Cikin kayanta ta laluba nan ta binciko y'an pieces enta da take amfani da shi tunda bata saba da pad ba.... Tsaf ta gyara jikinta ta dawo ta kwanta kamar ba ita ba..... *********** Sai bayan Maghreb sannan MA'U ta dawo a matuk'ar gajiye kamar wacce akawa duka haka ta shigo tana raba k'afa.. Da yake yawo ne kuma ita tasa kanta,duk da k'afar da take fama dashi,hakan bai hana mata zuwa yawoba..... ************ Shi kuwa ABBAN KHUBRA tunda ya fice daga gidan yaji bazai iya dawowa gidan ba... Haka yayi ta zamansa a waje,da yaje kasuwa ma k'odagonsa,bayan ya tashi k'in komawa yayi... sai dare ya koma gidan,shima sai da ya kintaci lokacin tayi bacci sannan ya nufo gidan..... *_~#TEAM KHUBRA.~_* *_REAL SMASHER._*🤞🏻😘 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *13/ąpril,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~__________________________~* *ADDU'AH YAYIN FITA DAGA GIDA.* _BISMILLAHI TAWAKKALTU ALALLAH WALA-HAULA WALA-QUWWATA ILLAHBILLAH._ _ALLAHUMMA INNIY A'UZHUBIKA AN-ADILLAH,AU'UDALLAH,AU'AZILLAH,AU'UZALLAH,AU'AZLIMA,AU'UZLIMA,AU'AJHALA,AU'YUJHALA ALAYYA.._ *ADDU'AH YAYIN SHIGA GIDA.* _BISMILLAHI WALAJNA,WA-BISMILLAHI KHARAJNA, WA-ALALLAHI RABBANA TAWAKKALNA._ *_~#HISNUL_MUSLIM.~_* *~__________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~__________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *1⃣3⃣* *T*ana shiga d'akin tayi shirim akan gadon tamkar kayan wanki,irin su MA'U irin matan nan ne da Sam basu da fasali a tsarinsu, bayaga d'an banzan son jiki da take da shi.... Kamar wacce aka mintsina haka tayi saurin mik'ewa tsaye tana raba ido... Wani durowa ta nufa,daga jikinsa kuma cikin wani d'an sak'o,ta mik'a hannu,poly bag en dake wajen ta janyo ta hau bud'e cikinta,tana fito da kayan dake k'unshe a ciki... Suphagetti ne da d'an dama dan idan basu fi 10 ba to zasu iya kaiwa hakan... K'waya d'aya ta d'auka ta nufi hanyan fita daga d'akin,a zuciyanta kuma tana sak'e²,har ta k'idasa ficewa... ********* Tana zaune ta idar da sallah ta rasa me ke mata dad'i a duniyarta,tunaninma yau kam tama kasa yinsa,duk jinta take kamar wata daban... Hankalinta gaba d'aya baya tare da ita a wannnan lokaci,tayi zurfi wajen tunaninta,tana son tuno wane garima dangin mahaifiyarta suke? Shigowar MA'U d'akin shi ya sata dawowa duniyarta babu shiri,cikin wani irin kallo ta jefeta da shi tana mai mik'o mata suphagettin dake hannunta,ba ko bayani ta sa kai ta fice.. Ita kam KHUBRA da ido ta bita dan zuwa yanzun ko dai bata gama sanin halin MA'U ba duka to tabbas ta san mafi yawan kaso daga halayentan.. Cikin sanyinta ta mik'e had'e da zare hijab en dake jikinta,ta fice tana sak'a da warwara... Har ta kammala bata sake jin ko da motsin MA'U ba,duk da hakan ba bak'on al'amari bane a gurinta,amma sai duk taji kewa na damunta,na rashin wani d'an adam... Juyewa tayi ta d'auka ta nufi cikin d'akin nata,tana ajiyewa ta juya ta fice... Hakimar tana kallonta amma ko sannu bare ta sa ran jin wata kalma mai dad'i,haka ta banzatar da ita,mik'ewa tayi ta janyo plask en.. Sai da ta gama k'oshi sannan ta shiga rafka mata kira... Cikin sauri ta shigo tana sunkuyar da kanta k'asa... Kwanon ta nuna mata,bata tsaya b'ata lokaciba ta sungumeshi tayi waje,sanin ko ta ce bata ci,kanta zata zalunta... Sai da ta tabbatar ta tsaftace duk wani abu da tasan tayi amfani da shi kafin ta nufi d'akin shirgi da a yanzun ya zama nata... Kwanciya tayi cike da son ganin mutumin ta na mafarki,tana wannan tunani har bata san lokacin da bacci yayi gaba da itaba... ********** Ko da MALAM BUBA ya shiga gidan direct d'akinsa ya nufa yana shiga kamar jiya da k'yar ya iya k'arasawa zuwa shimfid'arsa wanda baima tsaya tunanin ko lafiyaba ya kifa kamar wanda aka hankad'a,take wani nannauyan bacci yayi gaba da shi... ********* MA'U ce zaune cikin d'akinta,ta rafka tagumi,tunaninta ta yaya zata samu hanyar da kud'i zasu dinga shigo mata,dan kam wannan rayuwa lamarin yana damunta... Banda sak'a da warwara babu abunda take,zuciyoyinta biyu kowanne tana kawo mata shawaran da a ganinsu shi ne masalaha.... Ta tabbata idan akace zata ta'allak'a ne akan d'an abunda KHUBRA zata samu to tabbas tana cikin wahala,coz ta san halin yayarta da masifar son kud'i _(kunjifa wai kura ce za tace da kare maye)..._ Kafin wani lokaci mai tsayi zuciyarta ta gama rinjayarta,kwanciya tayi tana mai farin cikin samun mafita.... *IN THE MORNING* ******* KHUBRA dake tsaka da shara,ta d'aga kai ta kalli gurin da ta jiyo motsi,tayi matuk'ar mamaki da ta ganta a lokacin da batayi tsammaniba... ''Shin dama tana iya tashi da wuri haka,amma kullum sai ibada ta wuceta?''... Haka tayi ta tunanin abunda sam bashida wata fa'ida a gareta... Tana nan tana tunane² har bata san lokacin da MA'U ta gama shiryawaba,sai ganinta tayi ta fito hannunta rik'e da y'ar jakarta wacce akewa lak'abi da *_(JIK'ATA GUMIN HAMMATA)_*... Hannunta rik'e da leda ta fito tana jaan k'afarta da har yau bata samu an gyaraba... Naira #50 ta mik'a mata ''ki siyo garin kwaki''... Daga haka ta wuce ta fice,har tayi nisa ta dawo,KHUBRA dake sunkuye har tsoro abun ya bata dan bata ga lokacin da ta dawo ba,sai magana taji a bayanta.... _''Idan kinga ban dawo da wuri ba kina iya rufe gidan''_ Haka ta shud'a tayi gaba.... ******** Ko da ya farka da safe lokacin gari har ya gama haske,rana tana shirin mamaye sararin samaniya... Istighfari ya shiga yi,coz har aka idar da sallah bai san anayi ba,abunda a iya tsawon rayuwarsa yau ne rana ta farko da yayi rashin sallah a jam'i... Da matuk'ar k'unar zuciya ya mik'e ya fita don d'auro alwala... A tsakar gida ya iske LADIYO ta fito banda susar jikinta babu abunda take,kamar wadda tayi wanka da _karara..._ Ta gabanta ya zo zai wuce,cikin rud'ewa dan tasan zai mata fad'an rashin sallah a kan lokaci ne,ta hau fad'in ''MALAM barka da tashi'' Ba tare da tayi tsammanin zai amsa ba... Yana washe baki ya juyo yana kallonta ''Arrrhhh! hajajju LADIYO an tashi lafiya?''... Da mugun mamaki ta d'ago tana binsa da ido,sai dai tana yin wani tunani kuma ta waske tana murmushin mugunta _(hak'ansu ya cinma ruwa)_....... _#PLEASE FAN'S KUMIN UZURI DAN ALLAH NA RASHIN POSTING,UZURI NE YA MIN YAWA,DA YASA KO ONLINE BA NAYI,YAU KUMA NASO YIN TYPING EN BUH CIWON KAI YA HANA NI,IN SHA ALLAH ZA KUJINI ZUWA GOBE,DA YARDAR ALLAH..._ *_~#TEAM KHUBRA.~_* *_REAL SMASHER._* 🤞🏻😘 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *16/ąpril,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *ADDU'AR TAFIYA MASALLACI.* _ALLAHUMMAJ'AL FIY K'ALBIY NURAN,WAFIY LISANIY NURAN,WAFIY SAM'IY NURAN,WAFIY BASARIY NURAN,WAMIN FAUQIY NURAN,WAMIN TAHTIY NURAN,WA-ANYAMINIY NURAN,WA-ANSHIMALIY NURAN,WAMIN AMAMIY NURAN,WAMIN KHALFIY NURAN,WAJA'AL FIY NAFSIY NURAN,WA-A'AZIMLIY NURAN,WA-AZZIMLIY NURAN,WAJA'ALLIY NURAN,WAJA'ALNIY NURAN,ALLAHUMMA A'A'DINIY NURAN,WAJA'AL FIY ASABIY NURAN,WAFIY LAHAMIY NURAN,WAFIY DAMIY NURAN,WAFIY SHA'ARIY NURAN,WAFIY BASHARIY NURAN,ALLAHUMMAJ'ALLIY NURAN FIY K'ABARIY,WA-NURAN FIY IZAMIY,WAZIDNIY NURAN,WAZIDNIY NURAN,WAZIDNIY NURAN,WAHABLIY NURAN._ *_~#HISNUL-MUSLIM.~_* *~________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~__________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *1⃣4⃣* *B*akinta ta wage mai kama da k'ofar gari,hak'oranta kamar an shafa musu d'orawa... ''Lafiya k'alau MALAM'' Tana yi tana kwarkwasa kamar wata tsohuwar y'ar duniya... Shi dai binta yake da kallo kamar wani wawa,haka ya sungumi buta yayi band'aki.. Ganin haka yasa itama LADIYON ta nemi guri ta k'ame kamar soja tana jiran ganin me zai kuma biyo baya... Da mamaki take kallonsa yana alwala,mutumin da sallah bata wuce shi a jam'i amma shi ne zai yi sallah da wannan ranar... Jikinta taja ta shiga band'aki,har lokacin bai bar gurin ba,itama tayi alwala... Tana idarwa zata shiga d'aki taga ya biyo bayanta,da mamaki ta sake kallonsa,har ya shige d'akintan,ita kuma ta dafa masa baya... A kan abun sallah ta tarar da shi yana washe mata baki yace ''Yi sauri kisa hijab muyi jam'i'' Ita dai ido ne nata,haka ya jasu sallan har suka idar... After sun idar,ya shiga bata hak'urin abubuwan da yake mata,kamar wata uwarsa harda saka guiwoyinsa a k'asa.... Su LADIYO an samu abunda ake so,amma can k'asan zuciyanta tunani take akan yau shene shigowarsa ta k'arshe cikin d'akin nata,sai dai ta kasa tunawa... Jin da tayi ana shafa jikinta,shi ya dawo da ita duniyarta.. Kallonsa tayi cikin mamakin hakan,ta kasa cewa komi... ''Haba uwar gidan MALAM BUBA kice wani abu mana kinyi shiru'' Ita dai binsa take da kallo,shi kuma sai dad'a shige mata yake... Su LADIYO da jin haka,bata san lokacin da itama ta biyewa MALAM en suka ci gaba da shafar juna,har zuwa MALAM ya samu damar da yake nema a agurinta na cilla k'wallonsa a kwando.... Ihuuu LADIYO take tana fad'in ''Aradu MALAM kasan takan wanga harka,wayyoo dad'i,MALAM ci gaba''... Hannu yasa ya rufe mata baki,saboda surutun nata ya soma bashi haushi.. Ita kuwa sai dad'a mak'alo shi take,kamar wata k'wad'uwa.... 😂 ******** Duk wani aiki da za tayi sai da ta kammala shi sannan ta saka hijab enta.. Fitowa tayi daga gidan tana tafe cikin nutsuwa kamar yanda ta saba,haka har ta isa shagon,ta mik'a kud'in ya bata abunda zai bata,ta sake kamo hanya ta dawo... Ko da ta dawo gidan babu ruwa sosai,hakan yasa ta fita da bocket tayi ta faman jido ruwa a mak'otansu har sai da ta cika komai dake gurin... K'ofar gidan ta je ta kulle ta dawo,d'akin MA'U ta shiga ta kwanta a saman gadon MA'U tayi d'ai²,take kuwa baccin wahala ya d'auketa.... ********* Sai bayan komai ya lafa sannan LADIYO ta cika MALAM BUBA ta koma gefe ta kwanta... Shi kuwa MALAM sai bayan da ya gama biyan buk'atarsa sannan ya tuna inda yake da kuma k'yamar kusantar LADIYON a yanda take,riga kad'ai ya saka ya nufi band'aki yayi wankan tsarki.. 'Dakin ya sake dawowa,bai san dalilin da yasa yake jinsa wani iri ba,kamar mara lafiya... Kud'i ya zaro ya mik'a mata kan ta samu abinda za ta dafa a gidan,karb'a tayi,shi kuma ya juya ya fice daga gidan.... ******** Baccinta take ba tare da tunanin komai ba... Tayi nisa a baccin,ta hangoshi kamar kowane lokaci cikin fararen tufafi,binsa take amma ta kasa cin masa,hakan ya sa ta durk'ushe tana kuka mai tsanani.. Kiransa take HAYATEEY,amma ko waigowa baiba bare ya kalleta.... Hakan da yayi mata shi yasa ta fasa k'ara ta zube a gurin sumammiya.... ********** Can cikin garin SUMAILA cikin wani k'auye ta sauka ta ci gaba da ratsa hanya har ta billo wani farfajiyar guri... Gidane guda d'aya wanda ba shi da mak'ota ko k'waya... Tunkarar gidan tayi ta shiga k'wank'wasawa ganinsa a kulle.... Bud'e mata wata y'ar yarinya tayi,tana mai bata hanya... Murmushi tayiwa yarinyar ta bita suka shiga ciki... A wani d'aki aka sauketa ta nemi guri ta zauna tana jiran fitowar MALAMIN... Sai da ta shafe tsawon awanni 4 sannan mutumin ya shigo,daga shi sai dogon riga,duk ta k'udundune ga daud'a kamar ba jikin bil-adam ba... Zama yayi yana fuskantar ta... Ta bud'e baki za tayi magana ya d'aga mata hannu,alamar baya buk'atar tace wani abu..... ''Aikinki ba wani mai wahala bane,sai dai ta wace hanya kike so ta dinga kawo miki kud'in?''.... ''Koma mene ne MALAM tayi bai dame ni ba in dai zata dinga kawomin kud'i''.... ''An gama, sharad'in aikinki idan kika kuskure a cikin aikin da zan baki komai zai juya kanki''.. Tun bai k'arasaba tace ''Na amince'' Ta fad'a tana jiran ganin,me zai biyo baya... Nan take ta ciro wasu layu da kuma k'ullin garin magani,ya mik'a mata... ''Wannan ya nuna layun,zaki binnesu a tsakiyar hanyan da jama'a suke bi... Shi kuma wannan k'ullin ya nuna mata garin maganin,za ki barbad'a a bakin k'ofar d'akin da kija san za ta tsallaka.... Ki tabbatar ta tsallaka shi,saboda shi ne cikon aikin ki,zai sa mata farin jini wajen mutane,sai dai babu wanda zai zo da niyyar aurenta,zaki samu mahaukatan kud'ad'e ta dalilinta''...... Jin an ambaci mahaukatan kud'i ta shiga b'are baki,dan murna.... Kud'i ta fitar a jakar tata ta mik'a masa,ta masa godiya ta kama hanya,tare da alk'awarin dawowa... ******** Firgitan da tayi yasa ta farka,ga sautin k'ara da ya ratsa kunnuwanta wanda bata san daga ina yake ba,sai bayan ta farka ta fuskanci inda k'aran ya fito,ashe da tayi kenan ba iya cikin bacci kad'ai tayi ba har a zahiri tayi... Addu'ah tayi ta mik'e tad'auro alwala,ta jima tana neman sauk'in al'amura daga ubangiji,tare da kariyarsa a gareta... Sannan ta mik'e,ta d'auki garin kwakinta tayi waje..... Ko rabi bata iya ciba taji ta k'oshi,hakan yasa ta maida ragowar ta b'oye..... Tayiwa Allah godiya,ta sake kwanciya,tana tunani kan wannan rikitaccen mafarkinta..... Da yamma tana kwance a tsakar gidan,maranta taji tana tsunkulinta kad'an² take ta gane abunda yake shirin faruwa da ita,tashi tayi ta kintsa jikinta,ta dawo ta ci gaba da sauron kukan tsuntsaye dake kan bishiyar mak'otansu,haka har akayi sallan Maghre... Sai lokacin wani tsoro ya ziyarceta,take kuwa ta sake k'ulewa a d'akin MA'U.... ********** Cikin dare sosai ta iso,k'ofar ta shiga bugawa da iya k'arfinta... Jin bugun yayi yawa yasa KHUBRA ta fito ta bud'e coz ta gane mai bugun,sai a lokacin ta samu nutsuwa.... Duk wani shiri na MA'U ta gama k'udurce a daren ranar zata aiwatar da komai,hakan ne ma yasa ko gidan bata nufoba sai da ta aiwatar da nufinta... Lokacin gari ya dad'a yin shiru ta fito ta k'arasa abunda za tayi,ta koma zuciyarta wasai,sai kuma jiran ganin abunda zai biyo baya.......... #UHMMM!KU BIYONI DAN JIN YANDA ZA A K'ARKE.. LUV U..... *_~#TEAM KHUBRA.~_* *_REAL SMASHER._*🤞🏻😘 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *21/ąpril,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *ADDU'AR SHIGA MASALLACI.* _A'UZHUBILLAHIL AZIYM,WABI-WAJHIHIL KHARIM,WASUL'DANIHIL-K'ADIYM,MINASH-SHAI'DANIR RAJIYM,BISMILLAHI WASSALATU WASSALAMU ALAA RASULILLAH ALLAHUMMAFTALIY ABWABA RAHMATIK..._ *_~#HISNUL-MUSLIM.~_* *~________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~________________________~* _Ina mai bawa d'aukacin masoya wannan novel na *Y'AR GARUWA* hak'urin jina da kukayi shiru kwanaki da yawa,kumin afuwa na jina shiru tsawon wad'annan kwanakin,coz abubuwa sun min yawa shi yasa ban samu nayi posting ba,hope uzurina zai zama karb'ab'b'e..._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *1⃣5⃣* *C*ikin dare ta farka,sanadin mummunan mafarkin da tayi... Addu'ah ta jima tanayi,duk da babu halin tayi sallah,haka taita kai kukanta ga Allah akan neman sauk'i da sauyin rayuwa, wanda k'arshe sai da takai kusan asuba bata koma baccinba... Da k'yar ta samu wani nannauyan bacci yayi gaba da ita.... ********* Da misalin k'arfe 10:15am MA'U ta fito tana ta faman murna ta san ko ba komai yanzun kam ai tayi nasara.. 'Dakin da KHUBRA ke kwana ta nufa daga inda take a bak'in k'ofan ta lek'a sai dai duk iya hangenta bata gantaba,murna ta koma tana yi har da rawa na samun nasara... Har za ta koma d'akinta ta dawo tunowa da maganar da MALAMIN ya mata,akan idan har wacce akayi dominta ta tsallaka babu komai dan ta bi ta wajen... 'Dakin ta nufa tana son tabbatarwa,ai kuwa ta kunna kai cikin d'akin,tana ta murna abunta,sai dai abunda ta gani shi ya tsorata ta ta ko zaro idanu waje,ko me ta tuna kuma ta saki ranta... Cikin salo na bariki ta shiga tashin KHUBRA kamar da can haka take yi idan zata tashe ta.... Ko ita da kanta KHUBRAN sai da abun yaso ya bata tsoro,mamaki shimfid'e a kan fuskarta take kallon MA'U... ''Yar lele tashi maza kiyi wanka,ga abinci can na tanadar miki,maza taso kiyi wanka,zanje kasuwa zan siyo miki kaya,maza yi sauri kinji ko'' Ita maganganun MA'UN ma sun sa ta shiga wani irin shock,aiko haka taita binta da kallo kamar wata doluwa... Janta MA'U ta shiga yi,kamar k'aramar yarinya,har bakin band'aki ta kaita,tana murmushi ta turara... Ga KHUBRA kuwa bata gama mamakintaba sai da tasa hannu cikin ruwan wanka,nan taji shi da d'umi,wannan wane irin bak'on al'amari ne wannan kuma? Haka taita tunane²,tayi wankan ta fito,jikinta duk yayi sanyi.. Dai² lokacin MA'U ta fito daga d'aki tana fad'in ''Kiyi maza ki shirya kinji ko,zani kasuwa na dawo,kada kiyi girkifa,idan na dawo zanyi komai kinji y'ar lele'' Fuskanta a sake take ta faman zuba kamar lalatacciyar mota,har ta fice daga gidan tana magana wanda ita kam KHUBRA batama san me take fad'aba coz tayi nisa cikin duniyar tunani.... 'Dakin MA'UN ta shiga ta tarar da abinci a rufe a cikin plate da wani jug na robber mai d'an kyau... Bata tsaya b'ata lokaciba ta d'auko ta ajiye a k'asa ta shiga bud'ewa... K'amshi ne ya daki hancinta,tabi abun da ido,indomie ne da wainan k'wai a sama,sai turiri take,take ta shiga had'iyan miyau,haka ta bud'e jug en nan kuwa ta tarar da shi cike da tea mai kauri.... Ci tayi sai da ta tabbatar ta k'oshi tayiwa Allah godiya bisa ni'imar da yayi mata,na azurta ta da irin wannan abincin da tun da tazo garin bata tab'a cin kamarsa a dad'i ba... Sai da ta gama d'urawa cikinta d'a'aam sannan ta soma tunanin maganar MA'U... Tambayoyi dayawa taitayiwa kanta,sai dai babu amsa,ta barwa ranta koma mene ne ta tabbata shirin cutarta take,take kuwa ta hau kuka tana addu'ar neman tsari daga dukkan abun sharri.... Haka ta kusan wuni tana tunane²,shigowar MA'U da ta dawo daga kasuwa shi ya katse mata tunani,ta bita da kallon mamaki ganin yadda ta rik'o kaya a hannunta nik'i².... Tashi tayi za ta karb'a ita kuwa MA'U ta hanata,haka ta k'yaleta,guri ta samu ta zauna nan ta shiga fito da kaya tana d'agawa tana nunawa KHUBRA sai zuba take... Kayan marabarsu da babu d'aya,ita kuwa sai binsu take da ido daga KAYAN har MA'UN da ta siyo... ********* Tunda ya fita daga gidan ko waiwayarsa baiba haka ranar yaita uzurinsa a waje... Ita ko LADIYO tana ganin fitarsa ta zari mayafi sai gidan TABAWA nanfa suka shiga firar abunda ya faru tsakaninta da MALAM BUBA,bata b'oye mata komai ba ko da kuwa wasali haka ta sanar da ita hatta kwanciyar da sukayi sai da ta labarta mata... _(Gareku matan aure da y'an mata masu niyyar yin aure,ba ko wane sirri ake fad'awa k'awa ba,bare kuma har ki saki baki ki fad'a mata sirrin yadda kuka kwanta ke da mijinki,ko da kuwa ciki d'aya kuka fito,ahir d'inki da fad'in wannan sirri dan gujewa fad'awa a halaka,,,,,Allah yasa mu dace)... ameen....._ Haka ta kusan wuni a gidan LADIYO kafin daga baya ta tashi ta bar gidan... Ita kuwa TABAWA dad'i ne ya cika ta jin yadda LADIYO ta kwance mata sirrinta,tana rakata da harara tana tab'e baki,dan burinta bai wuce ganin LADIYON a k'asa ba..... ********** Ita dai kamar mai koyan kallon wani abu,irin wad'anda akayiwa aikin idanu haka ta zama ranar,duk inda MA'U tayi idanunta na kanta kamar zasu fad'o saboda kallo.... Da yamma kuwa tun bayan sallan la'asar MA'U ta sake sa KHUBRA yin wanka,cikin kayan da ta siyo haka ta sa wani riga da siket,da wani d'an siririn gyale,duk kunya ta hana KHUBRA sakewa haka suka fita,ita dai kallon kanta take kamar wata y'ar iska... Itama cikin shirinta suka fito,da tambaya suka nemi MALAMIN da yake gyaran targad'e... Ai kuwa sunyi masa bayani,MALAM na kama k'afar MA'U ya soma matsawa,ta shiga kururuwa,bige² take da hannayenta da k'afa... Amma MALAM bai saki ba,sai da yatabbatar ya gyara sannan ya saketa... Tun da aka soma gyaran MA'U na fara ihun nan,KHUBRA take ta b'oyayyiyar dariya,har kifawa tayi saboda dariya... Da k'yar take tafiya a da,sai gashi yanzun ta dawo normal,sai harare² da take uwa wani ya mata laifin.... Sai bayan da suka koma gida,cikin dabara MA'U take tambayan KHUBRA ''Yau kuwa kin fito daga d'aki?'' Kasa gane inda tambayan ya dosa tayi,ta tsaya tana kallonta kawai ''Baki gane ba ko?'' Kai ta d'aga tana jiran k'arin bayani ''Da safe fa nake nufi,kin fito ko kuwa sai da na shiga?'' 'Dan murmushi tayi ta kad'a mata kai,kafin tace ''A'a ban tashi da wuriba ai yau,sai lokacin da kika shiga sannan na tashi''... Ko kafin ta k'arasa MA'U ta mako mata wata uwar ashar da tasa tayi shiru tana k'ara kallonta cike da rashin yarda... Zagi ba irin wanda MA'U bata yiba a ranar,kamar za tayi hauka haka tayi²,da taga abun bai mataba kuwa k'arshe rufe KHUBRA tayi da duka,ita kuwa tana zaune inda take ko motsi bata yiba,har tayi ta gaji,dan kanta ta rabu da ita,ta koma gefe tana huci... Rasa dalilin yin hakan KHUBRA tayi mamakin da takeyi kuwa sai yanzun ta gano dalilin MA'UN na kulawar da ta ringa bata da safe... Abun duniya duk yabi ya dami MA'U,babu shiri ta tashi ta d'auki hanyar komawa k'auyen SUMAILA.... Da isarta kuwa babu b'ata lokaci MALAMIN ya k'araso,MA'U kamar za tayi kuka haka ta labarta masa abunda ya faru... Shiru yayi har ta gama,sannan ya sake mata bayanin da yayi mata tun farko,aikuwa saiga MA'U tana kuka,hak'uri take bashi kan idan da hali a karya abun... Shi kuwa yace mata ''Ai aikin gama ya riga da ya gama,sai dai kuma kiyi hak'uri''.... Wata k'arin muguntarma,bayan da MALAMIN ya bawa MA'U wancan aikin cewa tayi ''MALAM ina son a k'ara mata k'arfin sha'awa ta yadda duk wanda yazo mata da buk'atarsa baza ta iya jurewa ba'' Wannan maganar da MA'U ta tuna shi yasa ta b'arkewa da kuka,kamar ranta zai fita.. Shi kuwa MALAMIN take ya bata guri yana fad'in ''Har yanzun kina da damar yi mata wani aikin'' Nan ta shiga tunani,to idan za ayi wani aikin ai yana buk'atar kud'i,ita kuwa yanzu idan ba sata za tayiba ina zata samu kud'in aikin.... A ranta kam ta k'udirce ko za tayi yawo tsirara sai taga bayan KHUBRA... Nan ta lula duniyar neman mafita.......... *A YAU NE ABBANA YA CIKA KWANAKI 40 DA RASUWA,INA BUK'ATAR DAN ALLAH DUK WANDA YA KARANTA POSTING ENA NA YAU YA SANYA SHI CIKIN ADDU'AH DAN ALLAH..ALLAH YA MASA RAHAMA TARE DA 'DAUKACIN AL'UMMAR MUSULMI DA SUKA RIGAMU CIKAWA,ALLAH YA KYAUTATA K'ARSHENMU...AMEEN...* *_~#TEAM KHUBRA~_* *_REAL SMASHER._*🤞🏻😘 💠💠💠💠?💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *22/ąpril,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *ADDU'O'IN KIRAN SALLAH.* _IDAN MUSULMI YAJI ANA KIRAN SALLAH,ZAI DINGA MAIMAITA ABUNDA YAJI ANA FA'DA,SAI DAI BANDA *HAYYA ALAS-SALAH* DA *HAYYA ALAL FALAAH*,ZAI CE *LAA-HAULA WALA K'UWWATA ILLA BILLAH*._ *_~#HISNUL-MUSLIM.~_* *~________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~________________________~* _Ina mai godiya gareku Masoya da irin addu'o'inku ga mahaifinmu,Allah ya bar k'auna da zumunci... *SHUKHRAN OLL* 👏._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *1⃣6⃣* *J*iki babu k'wari ta d'ebi k'afafunta ta kama hanyar komawa gida,a ranta kuwa Allah ya isa take ta jawa KHUBRA,da zaran ta tuna sai ta sunkuya tana share k'wallan da ya tarun mata a ido.. Haka ta dawo gida,ita kuwa KHUBRA duk lokacin da zata tuna abun sai ya bata dariya,yanda MA'U taita fisge² da ana mata gyaran k'afa d'azun,ita ko dukan da ta mata bai sata jin haushin MA'UN ba,saima tayi dariya idan taga gilmawar MA'UN... Da tasamu sarari kuwa MA'UN ta fita ta zauna taita tuntsira dariya kamar wata sabon kamu... Shigowar MA'U gidan tana jan k'afafu,duk damuwa ya bayyana a fuskanta.. Kallon KHUBRA tayi da ta sunkuyar da kai k'asa kamar gaske,ae ko ta maka mata wata uwar harara,tana shigewa d'aki... Tun daga wannan rana MA'U bata sake fita ba,kullum tana d'aki kamar daddawa,sai da ta kai kimanin sati a gida ko zaure bata lek'a ba,abun duniya duk ya dameta ta rasa mafita... Yau tun data tashi take jin wata irin matsananciyar sha'awa na damunta,ta rasa yadda za tayi,ganin zaman bazai kai mata ba ta mik'e ta shirya cikin wasu riga da zani na wata jaan atamfa,babu laifi atamfan ya d'an mata kyau kad'an... Tun da ta fito KHUBRA ke k'unshe dariya dan har mantawa take da ita a cikin gidan coz ta san ba zaman gidan take ba... Ba tare da tayi mata sallama ba ta sa kai ta fice,mayafin jikinta tajaa ta rufe fuskanta da shi tana tafe kamar munafuka... Mai NAPEP ta samu,tsaf ta masa kwatance,dai² k'ofar gidan ya sauketa,ta shiga da sallamanta... Matar na zaune ta amsata,tana mata maraba,haka ta saki baki da fad'in ''Ina fatan dai kin ganeni koh?'' ''Haba ta ya zan mantaki kuwa'' Nan suka gaisa a mutunce,kafin MA'U tace ''Kinga tunda nace zan dawo Allah bai nufaba,sai yanzun,da yake na d'anyi jinya ne shi yasa kika jini shiru'' ''Allah sarki,Allah ya k'ara sauk'i'' Matar ta fad'a tana sauraron MA'U... ''To dama hajiya zuwa nayi na sanar miki,gobe idan Allah ya kaimu zan kawo yarinyar,sai ta fara aikin'' ''Allah ya nuna mana da rai da lapia'' MA'U ta amsa da ameen,had'e da yi mata sallama,ta tafi akan sai goben... 《《《》》》 Tun daga wannan ranar MALAM BUBA ya zamana zai kwanta da LADIYO a kullum babu fashi,ita kuma zata kwashe ta sanarwa da TABAWA.. Wasu munanan halaye da ta dad'a bayyanawa MALAM en shi yasa idan ya fice baya ko waiwayen gidan sai dare... Ko da suka koma wajen bokan,babu tsoron komai a tare da ita har bayyanarsa.. Kamar wancan lokacin ya zayyano musu abunda ya faru tun daga tafiyarsu kawo yau da suka dawo.. Kana ya d'ora da fad'in ''Dalilin dawowarku shi ne,Mijin naki ya fito miki da wani hali,idan yasa k'afa ya fita baya dawowa sai tsakar dare'' Nan taita d'aga kai kamar k'adange tana fad'in ''Haka abun yake'' Wata dariya ya saki mai kama da kukan jaki ''Zai dena da sannu,sai dai ki guji abunda zai had'a ku fad'a,yana da matuk'ar taurin kai,muma da k'yar muka shawo kansa,saboda haka a kiyaye'' Har za tayi sub'ul da baka na tambayan kud'in aiki sai kuma ta dafe bakinta tana tuno irin yadda sukayi wancan karon... ''Ku tashi ku bani guri,y'ay'an shaid'anu sun fara nema na... Babu shiri suka baro gurin cikin sassarfa,ba tare da kowacce tayi gangancin waiwayawa ba... A k'ofar gidan TABAWA sukayi sallama kowacce ta nufi gidanta... 《《《》》》 Shaf ta manta bata rufe fuskantaba,saboda tsananin murnan yadda ta samu nasaran taradda matar bata d'auki wata y'ar aikinba.. Burinta a yanzun bai wuce ganin KHUBRA a cikin mawuyacin hali ba,shi yasa ranta fes ta nufo titin da niyyar hawa mota.. Tsaye take tana kallon abubuwan hawa suna gilmawa a titin... Gani tayi an tsaya a gabanta,da wani mataccen babur,wani matsiyacin kallo ta bishi da shi,cike da jaraba ta d'ago idanu zata zazzage masa,karaf suna had'a ido sha'awa ya motsa mata fiye da ko wane rana da tayi shi a gida... Shiru tayi ta kasa magana,jikinta har rawa yake,lokacin da ta ganshi ''Hajiya ina zuwa ne?'' Yana magana yana lasar leb'b'ansa kamar maye ''Rijiyar lemo zani'' ''Toh Bismillah!hau muje na kaiki'' Ko jira batayi ya k'arasa ba tayi tsalle ta d'afe bayansa,shi kuwa ya figa machine en,tafiya kawai suke,MA'U gaba d'aya ta kasa samun sukuni,sai matsawa take jikinsa,tana ta faman mutsu² take masa a baya,shi kuwa yana jinta yayi shiru dama abunda yake nema kenan tunda d'an bariki ne,kuma abunda ya fito nema kenan,inda zai rage dare ba tare da kwabonsa yayi ciwo ba.. Sha'awanta sai dad'a k'aruwa yake fiye da farkon ganinsa,haka sai da ta kai gaba d'aya sun koma kan tank en machine en,shi dai yana jinta yayi shiru,har suka shiga cikin line en da gidan MA'U yake... A bakin k'ofa da zata sauka kasancewar maghreb yayi,da k'yar ta sauka shima sai da ta dafa shi sannan ta sauka,idanunta duk sun k'ank'ance saboda masifa... ''To Hajiya sallame ni na tafi,kinga machine en nawa ba wani Fitilar ce ke gare shi ba mai kyau'' K'afafuwanta take matsewa tana tsaye,duk ta shiga damuwa jin zai tafi Da damuwa take fad'in ''bari na kawo maka kud'in ina zuwa''... Shigewa tayi cikin gidan tana cije leb'e ta san idan har ya kufce mata wannan ta shiga tarama ba uku ba..... Kwanciya tayi a d'aki tana k'walawa KHUBRA kira,da gudu ta shigo har tana tuntub'e Ai kuwa MA'U ta dad'a rashewa a tana fad'in ''Yi sauri ki cewa mai mashin a waje,ya shigo bani da lafiya,ke kuma ba zaki iya d'aga ni ba'' Da damuwa KHUBRA ta tsaya tana mata sannu Tsawa MA'U ta kwad'a mata da yasa ta fice a guje.. Fitarta daga d'akin yasa MA'U tayi saurin cire kayan jikinta,ta lullub'a da bargo... Hankalinta a tashe tana fita ta ganshi tsaye ya kafe machine en gefe Tana haki take fad'in ''dan Allah bawan Allah ka temakamin bata da lapia karta mutu'' Kallon rashin fahimta yayi mata,can kuma yabi bayanta ganin ta riga ta shige.. Har tsakar d'akin MA'U dake k'udundune cikin bargo,tayi shiru kamar gawa ''Fita KHUBRA zamuyi magana'' Umarnin da MA'U ta bata kenan,tuni tasa kai ta fice daga d'akin,ta koma nata tana jimamin halin da take ciki... Fitarta ke da wuya MA'U ta mik'e,babu komai a jikinta,tana girgiza Wata dariya yayi irin ta y'an bariki ''Shegiya duniya,yo ae ba sai kinyi haka zaki sameni ba,da kin fad'ama da baki b'atawa kanki lokaci ba'' Ita dai MA'U babu baki,sai ido,take kuwa sabon saurayin nata ya shiga rud'ata da salo iri² kasancewarsa k'wararren d'an tasha.. Sun lula wata duniyar daban,bayan gurnaninsu babu abunda kake jin sautinsa na fita,sai da suka shafe tsawon awanni 5 suna abu d'aya,ba tare da MA'U ta gaji ba,shi kuwa dama haka yake so... K'arshe ma a gidan ya kwana,inda ya janyo machine ensa ya shigo dashi har cikin gidan... Tun da safe kafin KHUBRA ta tashi ya bar gidan,da alk'awarin zai dawo anjima tunda ta fad'a masa yau yarinyar zata tafi,amma yazo da wuri... Tun kafin rana ta take MA'U ta kira KHUBRA akan ta had'a kayanta,baiwar Allah tayi tunanin ko gida za a kaita,tana ta murna... Sai da taga ba tasha suka nufa ba,tad'an kalli MA'U a kaikaice tace ''BABA MA'U ina zamuje ne?'' ''Gidan uwarki da ubanki zamu,shegiya mai bak'in halin tsiya'' Ido KHUBRA ta fiddo waje,me yayi zafi? Ta tambayi kanta,ba tare da samun amsa ba...... *_~#TEAM KHUBRA~_* *_REAL SMASHER._*🤞🏻😘 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *23/ąpril,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *ADDU'AH BAYAN GAMA KIRAN SALLAH.* _A LOKACIN DA LADANIN YAYI KALMAR SHAHADA SAI MAI SAURARO YACE:-_ _WA-ANA ASH-HADU AN LAA ILAHA ILLALLAH,WAHDAHU LAA SHARIKALAH,WA-ANNA MUHAMMADAN ABDUHU WA-RASULUH,RADHIYTU BILLAHI RABBAN WABI MUHAMMADIN RASULAN WA-BIL ISLAMA DIYNAN.._ *BAYAN YA GAMA SAI YAYI SALATI GA ANNABI (S.A.W),SANNAN YA 'DORA DA FA'DIN...* _ALLAHUMMA RABBA HAZIHID-DA'AWATITTAAMMAH,WAS-SALATUL K'A'IMA ATIY MUHAMMADANUL WASILATA WAL-FADHIYLAH,WAB'ASHU MAK'AMAN MAHMUDANIL-LAZIY WA'ADTTAH,INNAKA LA TUKHLIFUL MIY'AD.._ *DAGA NAN KUMA SAI MUTUM YAYIWA KANSA ADDU'AH,DOMIN YIN ADDU'AH TSAKANIN KIRAN SALLAH DA IK'AMA KARB'AB'B'IYA CE..* *_~#HISNUL-MUSLIM.~_* *~________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *1⃣7⃣* *T*un da tayi shiru bata sake ko da tariba,har suka shiga unguwan tana ta bin ko ina da kallo kamar wacce take fadar shugaban k'asa,haka suka k'araso k'ofar gidan... Tana tsaye MA'U ta sallami mai NAPEP,tayi gaba ita kuma tana binta a baya har cikin gidan,da sallama suka shiga ita dai KHUBRA kanta na k'asa ta kasa kallon komai,duk kuwa da yanda gidan yake cike da abubuwan kallo.. A parlor suka tarar da ita ta hikimce kamar basarakiya,tana murmushi ta amsa musu,suka shigo suna zama,a k'asa kan rug KHUBRA ta zauna tana gaishe da hajiyan,ita ko MA'U ta hakimce akan sofa,suna gaisawa cikin sakin fuska.. Yanda MA'U ke k'asa da kai,sai ka rantse matar ta girme mata,ta mata bayani tsaf game da KHUBRA,lokacin da MA'U ta ambaci sunan KHUBRA matar ta bita da kallo hakan yayi dai² lokacin da KHUBRAN ta d'ago kanta.... Sai da taji wani mugun fad'uwar gaba,kan tsananin kyau d'an usul da ta gani a tare da KHUBRAN,a hakanma wai dan tana matsayin y'ar k'auye,ina kuma ga ace ta waye?'' Tunani iri daban² haka haka matar da ake kira HAJIYA MURJA take a ranta,a fili kuwa sai murmushin yak'e take uwa an mata dole... Cikin sakin fuska wanda da gani bai kai zuci ba,haka suka rabu da MA'U,ta mata alheri na Soap ne da su detergents a cewarta tayi wanki... Cike da murna MA'U ta amshe ta k'arawa k'afafunta wuta,ko sallama bata jira sunyi da KHUBRA ba.... Ga KHUBRA kuwa wannan ba bak'on al'amari bane da zai d'aga mata hankali,hakan da ta riga ta sani shi yasa ko damuwa batayi ba... Dawowar matar daga rakiyan da tayiwa MA'U tana dad'a mata godiya,tayiwa KHUBRA dake zaune wani wawan kallo,ko me hakan ke nufi? ohoooo.... Tana nan zaune ba tare da HAJIYAN tayi mata magana ba,ta sake hakimcewa a saman sofa tana watching T.V.... Da ihuuuuu suka shigo gidan,maimakon sallama da aka san d'an musulmi da ita,y'an mata ne su uku,sai yara biyu maza... Duka babbar bazata haura 18 yrs ba,inda mai bi mata nake tunanin zata kai 17 da gani tsakanin ta farko da ta biyu ba a sami wata tazara ba,sai ta ukun mai shekatu 14,sai namijin dake bi mata mai shekaru 12,in da na k'arshe d'an shekara 9 ke tsalle² uwa yaron biri... ''Oyoyo autanah'' HAJIYAN ta fad'a tana bud'e hannu.. Da gudunsa ya nufeta yana tab'ara,ita kuwa ta biye masa ''Kai hajiya dan Allah mu banda mu?'' Fad'in d'aya daga cikin y'an matan ''A'aaaaa ni na isa,haba uwar masu gida,taho nan maza uwata'' Duk abunda suke tana zaune ko tari bataiba,sai da sukai son ransu,sannan hajiyan ta turasu suje suyi wanka,dukansu suka mik'e suna bin hanyoyin d'akunansu.... Wani kallo ta mata cike da tsoro ta juya tana kallon hajiyan a zatontama gamo tayi,baki na rawa take tambayan hajiyan ''Hajiya wace wannan kuma?'' Sai lokacin Hajiyan ta kalli inda take nuna mata ''Oohhh!ASHNA sabuwan housemaid ne da mukayi,yau aka kawota,maza nuna mata inda zata na kwana'' Tana yi tana tana yatsina fuska,duk da fara ce ba zaka sata a sahun masu kyauba,sai dai kawai kud'i da suka hana a gano hakan... ''Tabbb!wallahi hajiya ba dani ba,sai dai ko waccen shashashar,da bata damu da darajarta ba'' ''To maza turomin ita,sai ta nuna mata'' Haka ta wuce tana hararar KHUBRA da bata sanma me take yiba Fitowar d'aya yarinyar alamun ranta a b'ace yake,ta zauna kusa da hajiyan tana fad'in ''Hajiya gani ASHNA tace kina kira na'' ''Yawwa yi maza ki nunawa waccan d'akin da y'an aiki ke zama'' Inda hajiyan ta nuna ta kalla,aiko cike da farin ciki ta k'araso kusa da KHUBRA tana mik'a mata hannu ''Suna na ZUHRA kefa y'ar uwa?'' Cikin halin ko in kula take maganarta,murmushi KHUBRA tayi mata tana mik'a mata nata hannun ''KHUBRA suna na'' Ko kafin hannunsu ya had'u da juna,hajiyan ta doke hannun KHUBRA,cike da masifa ta kewa ZUHRA fad'a ''Kinga ZUHRA ki kiyayeni wallahi bana son rawar kai,har zuwa yaushe zaki gane matsayinki?'' ''Nifa hajiya ba wani matsayi gareniba,naga dai duk d'aya muke a gurin Allah,wata k'ilama tafini a gurinsa,idan har ta fini kyautata masa'' ''To uwar tsari,bazan gaji da nuna miki hanya ba,saboda haka kibi ni a sannu,dan wollahi wata rana sai na b'allaki idan bakiyi a hankali ba'' Ta k'arasa tana zabga mata harara ''Ke kuma ta nuna KHUBRA dake sunkuye,ina son kisan cewa _BAKIN RIJIYA BA GURIN WASAN MAKAHO BANE_ So ki tsaya iya matsayiki,karki manta mun kawoki ne dan kiyi mana bauta,ina fatan zaki kula da aikinki''.. ''Wuce ki rakata d'akin y'an aiki'' Ta fad'a a tsawace Jiki babu k'wari ZUHRA ta wuce ita kuma KHUBRA na bin bayanta,har b'angaren y'an aikin gidan.. Suna shiga ZUHRA ta dawo kusa da KHUBRA tana fad'in ''Dan Allah kiyi hak'uri da duk abunda hajiyanmu za tayi miki,wallahi haka halinta yake,kaf y'an aikin gidan nan basa jimawa idan ankawo,dalilin halintane suke barin aikin'' Ta d'an saurara tana kallon KHUBRAN ''Kada ki damu in sha Allah zan zama mai hak'uri da duk abunda zan gani,na gode sosai da nuna kulawarki gare ni'' Sukama juna murmushi,daga nan ta taya KHUBRAN suka gyara d'akin tsaff,kamar ba shiba,sannan ta mata sallama ta koma cikin gida... 《《《》》》 Tun data fita daga gidan,take cin karo da maza iri² duk kuwa da yanda take ta rufe fuska,hakan bai hana maza sun biyo ta ba,kamar jiya haka ta samu wani Alhajin k'auye dan kuwa harda y'ar motarsa mai kama da zallan k'arfe,haka da dad'in baki da komai suka k'ulle,sai gidan MA'UN.. Kamar jiya haka yauma suka shek'e ayarsu,sai dariya suke b'ab'akawa,bayan sun gama,dai² lokacin da tasan wannan mutumin na jiya da ko sunansa bata sani ba zai zo,ta sallami alhajin da bawai ya gama kashe mata k'ishirwarta bane.. Har da y'an kud'ad'ensa ya kawo ya bata ita kuwa ganinsu ta dingayi kamar ya bata duniya... Yana tafiya kuwa mutumin na zuwa,da murnanta ta tare shi,tun daga tsakar gida suka fara watsi da kayan jikinsu,suna shiga d'akin kuwa ya shiga service en ta,tako ina ihunsu kake ji,abun ban haushi,tsawon awanni suka b'ata batare da sun gundiri juna ba,ranar da k'yar yayiwa MA'U dabara ya tafi,kan sai gobe,cike da k'aryar aiki gareshi... 《《《》》》 Tun kan gari ya gama wayewa,ta tashi ta shiga gyara gidan,duk da har lokacin bata san specific aikin ta ba,tsaff ta share ko ina duk kuwa da girma da yake da shi,sai harabar kad'ai da taga wani namiji yana sharewa.. Sakkowanta daga sama,kamar zata rushe matakalar benen,har ta k'idasa sakkowa,a kan sofa ta zauna tana jiran yaran su kammala sakkowa.. ZUHRA ce ta fara sakkowa,har k'asa ta gaida hajiyan,tana amsawa da k'yar kamar ba y'ar cikinta ba... ''Ina FATAHIYYA da ASHNA?'' ''Suna d'aki ne hajiya'' ''Ok!maza kiramin wannan yarinyar'' Ficewa tayi tana amsa mata A hanya ta ganta zaune kusa da shuke²n lambu tana ta kallon tsuntsaye dake gurin suna wasa,ita ko abun ya mata dad'i sosai yanayin gurin gwanin sha'awa.. Ta baya ZUHRA ta lallab'o ta rufe mata ido,murmushi tayi tana zare hannunta daga kan fuskanta,ta juyo tana kallonta,gaisawa sukayi ta hanyar musabiha da juna,ta nemi kusa da ita ta zauna suna hira jefi²,tun KHUBRA na murmushi kad'ai har ta soma bata answer,sosai suka saki jiki da juna... ''Laaaa!wallahi na manta'' Kallon ZUHRAN tayi tana fad'in ''Me kika manta?'' ''Hajiyace fa tace na kirawoki'' Ai tuni KHUBRA ta d'auki hanya,sai biyota ZUHRA tayi a baya A parlor ta tarar da Hajiyan da ASHNA na gefenta na dama,FATAHIYYA kuwa tayi pillow da cinyanta,suna zuba sangarta.. Kan rug ta zauna tana gaida Hajiyan,da k'yar ta amsa,kamar ana mata dole ta shiga yiwa KHUBRA bayanin duk wani aiki da zatana yi a gidan,kafin ta bata umarnin fara aikin daga ranan.. Babu musu kuwa KHUBRAN ta nemi a nuna mata kitchen,ZUHRA ce ta raka ta,tana d'an nuna mata wasu abubuwan da bata gane yanda za tayi amfani da shiba,cikin dabara KHUBRAN taita tambayarta abubuwan da suke so da wanda basa so,aiko taita mata bayani... Tana aiki ZUHRA na mata hiran yanda gidan nasu yake,kamar ta tambayeta,har ta kammala girkin duk da ba wani sanin abincin zamani tayiba tayi k'ok'ari,haka ta jeresu a dinning kamar yadda ZUHRA ta nuna mata,ita kuma tana tayata... Tare suka fita daga parlorn ASHNA na jin haushin KHUBRA da ta rasa dalilin hakan,ita ko ko ta kantama bata biba,coz bata san tana yiba... A guarding suka zauna k'afafunsu a cikin ruwan gurin,sai wasa suke suna dariya uwa sun saba dama can... ''Laaaaa!na manta ban baki labarin YAYANMU ba'' ZUHRA ta fad'a tana washe baki ''YAYANKU kuma,dama kuna da wani wa namiji?'' 'Ehhh! muna da amma baya k'asarma,karatu ya rabamu da shi,karki so kiga yanda yake sona sosai'' Tayi maganar cike da jin dad'in yanayin da take ciki ''Allah sarki,Allah ya dawo da shi lafiya,suka amsa da ameen oll'' ************ Kwanaki sun riski KHUBRA a cikin gidansu ZUHRA wanda bayan ZUHRA babu da wanda take sakewa,bayaga haka kuwa bata wani samun sakin fuska daga sauran y'an gidan bama kamar k'ananan da kana yi musu magana zasu maka rashin kunya komai girmanka kuwa,hakan yasa ko me za suyi KHUBRA bata musu magana......... Wannan kenan.... _#Haaaaaaa!Kunawa *MA'U* fatar ciwo ko,to maza ta jiku ni ba iya cetonku zanba,karta d'oramun k'afa na kasa tashi,dama bawani k'wari gare niba._ _Naga sak'onninku na addu'ah ina godiya sosai,Allah ya bar zumunci._ 👏👏 *_~#TEAM KHURA.~_* *_REAL SMASHER._*🤞🏻😘 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *25/ąpril,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *ADDU'AR BU'DE SALLAH.* _BAYAN AN YI IK'AMA_ _ALLAHUMMA BA'ID BAINIY WA-BAINA KHA'DAYAYA,KAMA BA'ADTA BAINAL MASHRIK'I WAL-MAGRIBI,ALLAHUMMA NAK'K'INIY MIN KHA'DAYAYA,KAMA YUNAK'K'AS-SAUBUL ABYADU MINAD-DANAS, ALLAHUMMAGHSILNIY MIN KHA'DAYAYA BIS-SALJ,WAL-MAA'I,WAL-BARAD.._ *_~#HISNUL-MUSLIM.~_* *~________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *1⃣8⃣* *K*imanin watanni biyar kenan da fara aikinta a gidan,tun daga ranan da tazo gidan ya zamana ita ke girki duk kuwa da ba wani iya girkin turawa tayi ba,acewarta irin wannan abincin a T.V take ganin ana nunowa kuma turawa keyi... Duk lokacin da ta fad'a kuwa nan ZUHRA zata sata a gaba tana dariya uwa ta samu shashatau en madina.... Yanda ZUHRA ke janta a jiki,abun har mamaki yake bata,ita ko kulawa da abunda hajiyanta ke mata bata yi,tun tana mata fad'a akan ta dena shiga sabgar KHUBRA har ta gaji,dan kuwa wata shak'uwa ce ta musamman ta shiga tsakaninsu kamar dama can sun san juna.... Duk tsayin wad'annan watanni kuwa ko da yaushe akace k'arshen wata yazo MA'U zata zo ta amshe kud'in aikin, KHUBRAN ko anini ba zata gani ba bare ta sa rai dasu..... 《《》》 Likaffa taci gaba a gurin MA'U danko a kullum a bata samu an tayataba idan ta fita ta yayibo mutum bakwai zuwa sama,d'an shaye²,mai babur ne,dama sauran jama'an gari,manya da k'anana binta suke... A kullum idan MA'U ta wayi gari takanji uwa k'ara mata sha'awa ake,shi yasa duk wanda ta samu ya biyota bata iya juran rasa shi.... Cikin shirinta ta fito zata gidan da KHUBRA ke aiki,dana kalleta sai da taban tsoro,saboda abun natama k'aruwa yayi,bayaga neman kasuwartata,fuskanta a kwailaye take ta sha mai,tamkar budurwa haka ta koma... Tana tsaka da rufe k'ofan d'akinta wani mutumi ya shigo gidan babu ko sallama... Itanma kallonsa tayi dan bata sanshi ba,tana fad'in ''Malam lafiya?'' ''Ehhh too lapiar kenan'' Sai da ya gama k'are mata kallo kafin da k'yar ya soma magana muryarshi a shak'e ''Ko kece MA'U motar haya?'' Sunan da ya ambata yasa na fiddo idanu waje ina jiran jin amsar da zata bashi.. ''Ehhh!me ya faru kake nemana?'' ''Dama nima maigidana ya aikoni na gano masa inda kike,sai kuma nayi sa'a na samekin'' Wani kallon sama da k'asa ta masa kafin tace ''Ban gane ba'' ''Hahahaha!ai ba buk'atar ki gane,yanzun dai mu shiga daga ciki kiji bayani tukun'' Ganin bata sanshi ba,zuciyanta kuma sai zarge² take kawo mata yasa tak'i bin umarninsa... Matsowa ya shiga yi kusa da ita,idanunsa a rine uwa wanda yasha wani abu... ''Ki bani had'in kai na yau,ina mai tabbatar miki idan har na komawa oga da labarin na sameki,zakiji dad'i sosai'' ''Wane irin had'in kai kuma kake magana'' Wata dariya yayi ta rainin wayo ''Kina b'atawa kanki lokacifa,mu shiga daga ciki kawai,ko zuwa biyu ne nayi na rage zafi,ina tabbatar miki k'aruwarki ce,dan oga ya iya kyautar girma'' Jin ya ambaci masu gidan rana,wanda kuma dalilin fitar tata kenan yasa ta washe baki tana fad'in ''Aaaaa! yo to ae yanzu naji batu'' Take ta bud'e k'ofan d'akin,suna shiga suka mannewa juna,dama masu jiran k'iris daga shi har itan... Yanda bai saurara mataba haka itama bata saurara masa ba,sai da suka dirji juna son rai... Tsawon awa uku sannan suka hak'ura badan sun gajiba,sai don kiran wayarsa da ake ta fama... Yana d'aukowa kuwa yaga OGA na yawo kan screen en wayan... Cikin gaggawa ya d'auka... ''Hello! OGA'' Daga d'aya b'arin aka hau fad'a kamar za a tsaga wayan ''Wannan wane irin rashin mutunci ne 'Dan Ladi zaka shuka ni tun d'azun,daga aikenka neman gidan kaje ka zauna'' ''Sorry mai gida,wallahi gidan ne ban samu ba,sai da k'yar yanzu hakama ganinan a hanya,kasan oga ba yanda za ayi nayi sanya gurin nemo maka ita a duk inda take kuwa'' Nan kan ogan ya huru,yana ta wani bada fad'i ''To don Allah kayi sauri,ni kaga na k'agu na ganta,saboda masifar k'ishirwarta ke damuna,idan ban sauke yauba da matsala'' ''An gama oga,ganinan k'arasowa,ai kamar ka biya buk'atarka ka gama'' Yana fad'an haka suka shek'e da dariya duka suna ajiye wayar... ''Shege oga,idan yaga mace kamar ayu haka yake da son matan tsiya,dan shi har yafi d'an akuya'' Ya saki wata uwar dariya yana kallon MA'U da tayi laga² akan gadontan,duk ta wani bud'e k'afafu... ''Yahhh!ko kina buk'atar k'ari ne? naga kin kasa tashi'' Bata kulashiba tayi shiru,dan kam ita kad'ai tasan me take ji,duk lokacin da akace an gama biyan buk'ata da ita,nan take wata sabuwar sha'awar zata bijiro mata,kai ita kam ma batak'i ta kwana ta yini ana mata service ba.... Haka ya gaji da surutunsa ya fice,baifi minti talatin ba suka k'araso har cikin gidan,da wani k'aton mutum gashi da uban timbi.... Tana daga kwance yanda ya barta haka suka dawo suka tarar da ita,sai mayafi data d'an rufa ajikintan... Su oga anga gara babu shiri ya kalli yaron nasa ''Dan ladi,zaka iya tafiya ni zan taho daga baya'' Yanayi yana sid'e leb'e,an gama oga,ya fice yana zabga masa harara.. Idanun MA'U a rufe saboda yanda ta jefa kanta a wahala... Shiko shirgegen k'aton nan ya nemi guri ya kime kayansa,ya shiga aiki ba ji ba gani... MA'U banda ihu ba abunda take,dan kuwa wannan mutumin maimakon ya nemeta ta gaba,shi biyu ya had'a,sai da ya gamsu son ransa sannan ya kyaleta.. Aiko MA'U ta had'u da gamonta,ta kwanta sai numfashi take fiddawa da k'yar.. Ganin ya samu abunda yake buk'ata,da murnansa ya duma hannu a aljihu.. Naira dubu hamsin ya damk'a mata,wanda tajisu kamar an mata bushara-..... Shi kuma ya fice da alk'awarin dawowa zuwa dare............ *_~#TEAM KHUBRA~_* *_REAL SMASHER._*🤞🏻😘 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *28/ąpril,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* _SUBHANA RABBIYAL-AZIYM ׳._ _SUBHANAKALLAHUMMA RABBANA WABI-HAMDIKA ALLAHUMMAGHFIRLIY._ _SUBBUHUN,QUDDUSUN,RABBUL-MALA'IKATI WARRUUH.._ *_~#HISNUL-MUSLIM.~_* *~________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *1⃣9⃣* *T*ana nan kwance kamar kayan wanki,ya fice daga gidan,duk da uwar wahalar da tasha,ko cikakkiyar awa ba ayi ba,ta soma jin wani feeling na dad'a matsarta,tana cikin wannan hali ko 'DAN LADI ya dawo sai sauri yake,har da tuntub'e dan kam shifa ya ga banza irin wannan gara haka,baiga ranar bari ba,a cewarsa ''shi yayi oga yayi''... A hankali ta d'ago jin takun tafiya,aiko idanunta na arba da shi ta kai masa wata wawar cafka,uwa wacce take tsoron zai kufce mata,shima da dama abunda ya dawo da shi kenan,ya shiga lashe leb'e,take ko suka sake komawa ruwa... 《《》》 Duk wani aiki da tasan ita za tayi shi ta kammala shi da wuri,ta koma wajen lambu tai zamanta,sai kallon tsuntsayen dake sauka gurin take tana ta murmushi abunta... Lokacin sallah nayi ta nufi tap en gurin,anan tayi alwala ta nufi d'aki tayi sallah,ta sake komawa ta zauna,kasancewar y'ar hirar tata bata nan,tana skul... Wajejen k'arfe 3 saura ko ta jiyo ihun su HANEEF suna guje² daga ji ko tasan dawowarsu kenan,tana zaune taji an rufe mata ido da hannu da ji ba sai ta tambaya ba,tasan ko wace ta mata haka,saboda sun saba zuwa wannan lokacin... Murmushi tayi tana fad'in ''Haka dai kullum kike gani,a zatonki ba zan gane ba ko?'' Dariyar itama tayi tana zare hannunta ta zagayo ta zauna kusa da ita,nan ko suka hau hiransu kamar kowane lokaci... Har kiran sallan asr suna wajen,kafin suka mik'e suna barin gurin dan gabatar da sallah.... Malamin da HAJIYA MURJA tasa a nemo na islamiyya ne ya shigo da sallamarsa ya gaida hajiyan,ita ko KHUBRA lokacin tana kitchen had'a abincin dare,duk maganar da suke tana iya jiyo su,amma ba wai su en take sauraroba,aikinta take kasancewar yanzun takan gwada girkin turawan,saboda yadda ZUHRA ke bata gudunmawar kamo mata tashoshin da ake girkie² idan HAJIYANSU bata nan,aiko da yake tana da basira kuma ZUHRAN kan fassara mata abubuwan da suke da hausa,hakan yasa ta bata littafi da biro da kanta take rubutawa da ajami,saboda KHUBRAN tayi makarantar allo,shi yasa takan iya rubutu da ajami... Idan ta gama ta kai abunta ta b'oye a cikin kayanta,duk ranar da za tayi girki idan tana son gwadawa haka zata d'auko taita karantawa har sai ta haddace komai,da haka zata shiga kitchen,cikin ikon Allah kuwa idan tayi girkin zaka tarar yayi dai².Ta wannan b'angaren ZUHRA ke mugun yaba mata,kuma takan tsaya tana kallon yadda take tana taimaka mata da mik'o wancan da wannan.. Aikinta take tayi,kasancewar yau ba y'ar tayin nata,har ta kammala bata shigoba,ta gyara komai ta mayar da komai wajen zamansa,ta fito kenan zata fita taga ASHNA ta shigo fuska babu walwala tana ta faman cika,hanya ta bata ta wuce kafin itama ta wuce ta nufi barin parlorn... ''Ke zo nan'' Ta juya taga ita ASHNA ke kallo,hakan ya tabbatar mata da cewa da ita take,kanta a k'asa ta je inda take... ''Kije d'akina zakiga kayan wanki na ki d'ebo ki wankemin,bani da kayan sawa'' ''Kiyi hak'uri amma wanki baya cikin aikin da zanyi muku'' ''Ke don uwarki har kin isa nasaki abu ki ce baza kiyiba?,wallahi baki isaba,kuma wanki kam sai kinmin'' Tana gama fad'in haka tayi hanyar d'akin HAJIYA MURJA tana rafka mata kira uwa wata sa'arta ba mahaifiyarta ba.. ''Ya akayi y'ar lele?'' Ta tambayeta tana fitowa daga toilet.. ''Hajiya wai waccan yarinyar ce na ce tamin wanki ta tsaya tana nenan zagina'' Uwa za ta fashe kan haushi... ''Kan uba ita d'in banza tak'i yi miki wanki,y'ar waye ita?dawa take tak'ama? da har zaki sata abu tak'i,maza matsa na je naci mata uwa'' Tafice uwa zata tsaga ginin da take takawa... Har ta fita ta dawo,ta d'auki ruwa ta sha,tana fitowa ko sukayi arba da hajiyan, ''Ke don ubanki har kin isa a saki aiki a gidan nan kik'i yi?wace ce ke da zaki k'i?'' Sosai taji wani abu na sauka a ranta jin zagin da akayiwa mahaifinta da take tsananin so a duniyarta,duk da ranta ya b'aci da zagin,haka ta daure ta soma bawa hajiyan hak'uri ''Wollahi hajiya ba yi ne bazanba,kawai cewa nayi mata tayi hak'uri wanki baya cikin aikin da zanyi a gidan nan''... Wani mari da hajiyan ta mata shi ya katse mata magana,take ko ta dafe gurin tana dad'a sunkuyar da kanta.. ''Maza ki wuce ki d'ebo kayan,duk da babu shi a yau na k'ara miki dashi acikin aikin naki'' Tana gama fad'a ta juya tayi wucewarta tabar KHUBRA da dafe da kunci... Ganin babu sarki sai Allah ta rarrashi zuciyarta,ta wuce zuwa d'akin ASHNAR,tattara kayan tayi kaf closet enta babu wani kaya da ba a b'ata ba,haka taita jido su tana fito da su har ta kammala... A washing machine taita sawa tana wankewa,da yake tana taya ZUHRA wani lokacin,kuma itama takan wanke nata,haka ta b'ata lokaci mai tsawo tana fama da kayan... Tana cikin wanki ta jiyo muryan ZUHRA na kiranta,tana daga cikin toilet en ta amsata,aiko ta shigo... Da mamaki ta kalleta tana fad'in ''Me kuma ya had'oki da wanki yau?'' Murmushi kad'ai tayi,bata iya cewa komaiba,haka taita fama da wankin ita kuma ZUHRAN na tayata matse kayan,tsaf ta gama lokacin ana kiran sallan isha.. Sai da sukayi sallah tukun sannan suka shanya kayan,suka ci gaba da fira a d'akin KHUBRAN haka suka raba dare suna fira,sannan ZUHRA tayi mata sallama ta tafi d'aki,itama ko nan ta kulle k'ofa ta kwanta zuciyarta fal tunanin makomar zamanta a gidan.... 《《》》 Sai da suka raba dare suna abu d'aya dukansu babu wanda yayi tunanin yin sallah,suna ta faman aikata masha'arsu... Dan kansu kuma suka hak'ura da juna badon sun gajiba,don dukkaninsu gwanaye ne a harkar,kuma kowa nunawa d'an uwansa yake yafi d'ayan,sai da suka raba dare a haka,sannan kuma bacci yayi gaba dasu suna hakan,ba tare da sun tsarkake jikinsu ba bare gaida mahalicci... 《《》》 Shigowarsa gidan yaji kansa yana sara masa,take ko ya dafe kansa yana mai nufar d'akinsa ya kwanta ba tare da addu'ah ba bayan a da ya saba baya tab'a kwanciya bai yi addu'ar ba... Tayi nisa cikin baccinta ta ji ana shafata,cikin magagi take magana,amma bai kulata ba yaci gaba da abunda yake jin abun yayi nisa kuma babu halin a daina yasa ta bud'e ido,wa zata gani?? Cikin firgici ta furta ''B...O....BO....K.A.....'' Bakinta har sark'ewa yake gurin maganar,shiko ya d'ora hannunsa a baki yana mata alamar tayi shiru.. Babu shiri ko ta ja baki ta tsuke,bata kuma furta ko a ba,haka ya rabata da ilahirin kayan da ke jikinta ya shiga amfani da ita,duk ilahirin jikinta ya mutu saboda tun da ya zo ya shafata,jikintan ya idasa mutuwa ta gagara tab'uka komai,har ya gama biyan buk'atarsa wanda ba shi ya k'yaleta ba sai gabanin b'illowar alfijr... Kallonta yayi yana dariya wacce ta cika d'akin ''Kiyi maza kije d'akin mai gidanki,kisan yadda za kiyi ku samu wata alak'a ta shiga tsakaninki da shi a yanzun kafin b'illowar alfijir idan kikayi haka,duka buk'atunki sun gama biya kenan''...... Yana gama maganar ko ya b'ace,ta neme shi ta rasa,take ko ta ja zani tayi waje,tana shiga d'akin MALAM BUBA ta yi karo da shi kwance yana bacci,ai bata jira komai ba,ta sa k'arfi ta mirginashi ta ko hau shafa shi kamar yadda boka ya mata... Da yake bai da magagi ya bud'e ido,suna yin arba da juna tayi cilli da zanin jikinta... Wani sara masa kansa yayi,yayi saurin runtse idanunsa yana damk'e kansa,ganin haka LADIYO ta birkice tana fad'in ''Sannu MALAM ciwo kan ke maka?'' Kai ya kad'a mata bai ce komaiba,ita kuma ta fice tana nemo garin magani zata jik'a masa dan burinta bai wuce aiwatar da bayanin boka ba... Kaf sai da ta hargitse d'akinta kan binciken magani amma bata ganshi ba.. Wani uban tsaki ta doka tana ficewa zuwa d'akin MALAM en... Shiko tana fita wani bacci ya sake d'aukarsa,duk budirin da take bai sani ba... Dai² zata shiga d'akinsan taji masallacin dake unguwan ladanin ya fara kiran sallah na biyu,alfijirya keto kenan,tuni LADIYO ta buga wani wawan tsalle tayi cikin d'akin MALAM en.... 《《》》 Cikin daren ko a b'angaren KHUBRA haka ta tashi tayi alwala tahau jero nafilfili tana dad'a kai kukanta ga rabbis-samawat.. Har aka kira sallah tana kan abun sallanta,sai da tayi sallah sannan ta d'an kwanta,aiko take bacci mai dad'i ya sake d'aukanta... A furgice ta farka tana kallon yadda gari ya soma haske,cikin sauri ta watsa ruwa ta fita tayi kitchen,abinci ta d'ora mai sauk'in dahuwa,cikin lokaci k'ank'ani ta kammala komai har girkinsu HANEEF da yake su biyu ne ke tafiya da abinci,ta gama had'a musu a lunch-box ensu.. Sai lokacin nutsuwa tazo mata,ganin ta kammala cikin lokaci k'alilan,tayiwa Allah godiya,sannan ta fita ta shirya musu dinning.. A cikin kitchen en ta ci nata abincin,tana gamawa ta hau wanke².. Dai² lokacin ZUHRA ta shigo,sad'af² ta biyo ta bayanta ta rufe mata ido... Murmushi tayi tace ''Habaaa ZUHRA kinma mai dani wata abar tsokanar ki kenan,kina tsammanin bazan gane bane?'' Tayi murmushi itama suka gaisa,a gurguje ta mata sallama ta fice daga kitchen en... Suna fita ba jimawa itama ta fito ta tafi d'aki,ta kwanta tana tsaka da tunani bacci ya d'auketa dan kuwa dama baccin take ji....... *_~#TEAM KHUBRA~_* *_REAL SMASHER._*🤞🏻😘 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *3/mąყ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* _Masoyana a ko ina kuka kasance bazan iya mantawa da k'auna,halacci tare kuma da kyatatawarku gare niba,tabbas kun nunamin karamci wanda ba zai tab'a gogewa a cikin raina ba har sai bayan bana numfashi,Allah ya bar k'auna tare da zumunci.._ N A G O D E _Sosai da sosai,Allah ya barmin ku,duk inda kuke ina tare da ku da izinin Allah... *#1 luv my peps..*_ *~________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *2⃣0⃣* *K'*afafunta saboda tsabar kid'imewa da tayi har neman kasa d'aukarta suke,kamar an cillota ta fad'o d'akin aiko bata jiraba ta afka kan MALAM dake ta sharara bacci abunsa... Shafa shi ta shiga yi shi ko maimakon ya farka kamar yadda yayi d'azun saima dad'a gyara kwanciya da yayi,yana sakin numfashi abunsa... Haushi duk yabi ya cika mata zuciya,haushin rashin farkawarsa yasa ta kirb'a masa wani naushi aiko take ya bud'e ido,murmushi ya mata ya sake kulle idonsa yana mai dad'a gyara kwanciyarsa...... Kamar mahaukaciya ta fice tana sosa jikinta........ 《《》》 Tsaf suka gama shek'e ayarsu a daren,har safiya suna mak'ale da juna... Yanayin kwanciyar da suka yi kai da gani kasan ba shiryawa baccin suka yiba,dan kam da gani kasan suna tsaka da harka baccin yayi awon gaba da su..... Ko da ta farka lokacin har gari ya gama haske,sannan ta bud'e idanunta da suka mata nauyi... Jiki ba k'wari ta fita tayi wanka,bata tashe shiba dan kansa ya tashi yayi wanka,lokacin ko a takure ya ganta wanda ita kad'ai tasan halin da take ciki... Sai da ya gama shirin ficewa tukun ya dawo ''Yahhh!d'an kawo wani abu mana'' Da rinannun idanuwanta ta kalleshi tana neman k'arin bayani... ''Ko zaki cemin oga bai sallamekiba?'' ''Ohhh!kuma nufinka ni zan baka wani abu cikin kud'in ne?wato baya ga biyan da na maka har wani sabon tukuicin kake nema?'' Dariya yayi irin tasu ta y'an duniya,kafin ya juya yana nufar hanya yasan kam duk inda ya kai da son duniya MA'U ta fishi,haka ya fice yana fad'in ''Sai kin ganni'' Bata ko d'aga ido ta kalleshi ba bare ta bashi amsa......... 《《》》 Ko da ta farka bata wani b'ata lokaci ba ta koma bakin aikinta,har ta kammala ta fito da niyyan komawa b'angarenta.. A parlor ta tarar da ita tayi shirim cikin sofa,har zata fita ta kwad'a mata wata tsawa,ba shiri KHUBRAN ta dawo dan ita kam a yanzun baza ta so abunda zai rabata da gidan ba,dan ko shi ne rufin asirinta a wannan halin da take ciki... ''Wanki yana nan ya taru,saboda haka kiyi maza ki soma'' Shiru tayi ta kasa magana,zuwa wani lokaci kuma ta mik'e uwa kazar da kwai ya fashewa a ciki.Haka ta jido kayan masu uban yawa sai wari suke uwa masu kayan basu san wani abu mai kama da turare ba,ko da ta kaisu bakin washing machine en gani tayi kayan sam ba zata iya wanke su iya yau ba,dan ko kaya ne har na mutum biyar,bata b'atawa kanta lokaci gurin tunani ba ta hau abunda tasan shi zai fishsheta,tun tana na marmari har ta gaji.A haka su ZAHRA suka dawo suka tarar da ita,ko kallon arzik'i bata samu daga gurin ASHNA da FATAHIYYA ba.. ZAHRA kam dama tuni ta riga kowa shigowa,nan tai ta mata sannu,haka suka shiga ciki... Ko cikakken mintuna talatin batayi ba ta fito ta dawo gurinta aiko tare suka ci gaba da aikin shanya,har malaminsu na islamiyya ya zo,a nan ne ta barta ta tafi,har suka dawo bata kammala ba,k'arshe dai yinin ranar haka ya shud'e mata tana abu d'aya.. Wajen k'arfe goma na dare ta tattara ta ajiye su akan ta k'arasa idan Allah ya kaimu washe gari........ Rayuwa ta mik'awa KHUBRA cikin wannan gida,wanda iya wannan lokacin babu wani abu dake shiga tsakaninta da y'ay'an gidan,ta kame kanta had'e da rik'e matsayinta na y'ar takala,duk wani aikinta tana gama shi take barin cikinsu ta koma guarding tai zamanta,mafi yawancin lokaci nan ne gurin da ke d'ebe mata kewa,musamman idan ta tuna ABBANTA ko MAMANTA da bata tashi tayi rayuwa da ita ba... Cikin sauri² ta fito zata shiga cikin gidan,karo suka kusa yi da ZAHRA,da saurinta kuma ta tsaya tana kallonta duk sai murna take uwa wacce akama wata gagarumar kyauta,kallonta ta tsaya yi... Da sauri ZAHRA ta rik'eta tana jan hannunta suka nufi kitchen,aikinta ta fara suna ta hira,duka yau tana kula da yanayin ZAHRA wani murna take tayi ita kuma tak'i tambayan dalilin,suna ta aikin su,can ZAHRA ta d'ago tana kallon KHUBRA... ''Wai kam sis kin san wani abu?'' Kai kad'ai ta kad'a mata kafin ta bud'e baki tayi magana ZAHRA ta katse ta da fad 'in ''Cikin month ennan YAYANMU zai dawo fa'' ''Eeyyahh!Allah dawo da shi lafiya,yasa ya samo abunda yaje nema'' ''Ameen dear,aiko zai sha labarinki duk ranan da mukayi waya'' Ita dai KHUBRA bata sake magana ba,ta ci gaba da aikinta,ZAHRA kuwa nan taita bata labarin YAYAN nasu,wanda har zuwa yau bata tab'a tsintar sunansa ba.. Har suka kammala,ZAHRA nata mata surutu,ita ko sai dai tayi murmushi yanayin yanda suke rayuwa da yadda ZAHRA take bata labarin irin rayuwarsu abun sosai yake bata sha'awa,har wani lokaci ma ta kanji inama itama tana da d'an uwa,duk lokacin da ta tuna haka takan yi kuka sosai... *SOME WEEKS LEAP.* Da sanyin safiya ta tashi,bata b'ata lokaci ba ta shiga kitchen,tunanin irin girkin da za tayi ta hau yi,dan kam tun jiya HAJIYA MURJA ta sanar da ita suna da babban bak'o,saboda haka tana son tayi girke² kaloli da yawa had'e da drinks na gargajiya,coz ta san bak'on baya son tamalli da kayan gwangwani... Tana cikin tunanintan ZAHRA ta shigo da saurinta,sis bafa muga ta zama ba,kinga tunda ke kad'aice barin fasa binsu airport,muyi abunda ya kamata,nan ko suka hau aiki ba ji bare gani,suna yi suna hiransu... Tsawon awanni da dama suna ta aikin kafin suka kammala,ficewa suka yi bayan sun gama shirya table kafin kowa ya kama hanyarsa... *SOME HOURS LATER...* Wani bak'in PRADO ne ya Parker a haraban gidan,cikin k'asaita aka bud'e k'ofan ko kafin ya bud'e ya fito sai da ya d'auki lokaci kafin ya ziro k'afarsa ya fito,cikin k'ana nan kaya wanda suka matuk'ar amsarsa uwa bature,gashinsa ya d'an yi tudu ta gaba sai shek'i yake da gani kasan yana shan gyara,idanunsa saye cikin sunglasses bak'i na GUCCI,komai yayi kyau yake masa,cikin takun k'asaita ya soma tafiya,har cikin parlor da ya sha gyara.A baya suka bishi har cikin parlorn sai rawar kai ASHNA da FATAHIYYA suke zubawa,shi kam yana gaba bai ko kula ta kansu ba,a zaune suka tarar da HAJIYAN sai wani dare baki take tana dariya had'e da fad'in ''Oyoyo my son'' Fuskarsa d'auke da murmushi da ya dad'a k'awatar da ita,ya amsa yana zama cikin sofa.. Cike da ladabi uwa ba wanda ya fito daga k'asar turawaba ya gaidata,tana amsawa fuskarta da fara'a wacce ban tab'a zaton tana da ita ba... 'Dakinsa ya nufa cike da gajiya,yana shiga wani sanyayyen k'amshi ya doki hancinsa,take kowace gab'a ta jikinsa ta amsa,jinsa yake uwa an masa duka,da k'yar ya k'arasa kan bed,aiko ya zube saman bed yana dad'a shak'an k'amshin turaren kasala na dad'a saukar masa a jiki,jin abun zai masa yawa yasa ya mik'e da k'yar ya iya nufar toilet,ya jima ciki kafin ya fito,ko minti biyar bai ba ya shirya cikin singlet fari da boxer,ai ko ya haye saman bed take baccin gajiya ya kwashe shi... Tun bayan da suka gama aikin suka k'ule a guarding sai fira suke suna dariya abunsu uwa ya da k'anwa duk da baza su wuce sa'annin juna ba... Sam basu ji shigowar motor ensu ASHNA ba,sai shewansu suke KHUBRA na bata labarin k'auyensu,ita ko ZAHRA sai kwasar dariya take... Three hours ya d'auka yana baccin gajiya kafin ya farka,jin cikinsa fayau yasa cikin sauri² ya sake watsawa jikinsa ruwa,jallabiyya ya zura,sai da yayi sallah sannan ya fito,suna zaune cikin parlorn su HANEEF duk sun cika gurin da hayaniya,ganin fitowansa yasa take suka shiga hankalinsu ba tare da ya furta ko a ba,k'ala bai ceba amma gaba d'ayansu kowa ya k'ame kamar doll... ''MAMA ni kam ina Sis ena?'' Tab'e baki tayi kafin cikin b'acin rai ta iya furta ''Tana can tare da wannan shashashar yarinyar'' ''Wace wannan kuma?'' Yayi maganar yana yamutsa fuska... Saboda tasan halinsa na rashin son magana yasa tace ''Wata ce'' Daga haka ko ta bar maganar ba tare da ta sake furta komai ba ta ja bakinta tayi shiru... ******* ''Laaa!sis kinga lokaci ya tafi nasanma yanzu haka BB ya dawo,taso muje dan Allah'' ''A'a y'ar uwa ki je yanzun zan biyoki daga baya '' ''Ba wani nan nasan ba zuwa za kiyi ba'' Murmushi kad'ai tayi,ita kuma tayi saurin barin gurin tana fad'in ''Sai na ganki duk da ba yarda nayi akan za kizo ba'' Tana tafe da d'an gudunta ta shiga parlorn,idanunta na sauka kansa ta fasa wani ihu da gudu kuma ta fad'a jikinsa.... Jin an fad'o jikinsa yasa ya kalleta,sai murmushi take dokawa,shi ko ya had'e fuska yana fad'in ''Matsamin a nan,ai ke kam fushi nake da ke'' ''Wayyoo YAYANAH dan Allah kayi sorry kar kayi fushi da ni,kasan duk duniya bana k'aunar naga kayi fushi da ni,ko so kake nayi kuka?'' Ta fad'a tana narke fuska za ta masa kuka ''Haba mana sis ina kika b'oye?ko kije tarona kuma na dawoma ban saki a idona ba why?'' ''Ammm!YAYANAH Allah ko aiki mukayi shi yasa kaga banje taroka ba,kaima kasan ba haka kad'ai zan k'i zuwa ba,aiiii dai ka hak'ura ko?'' Tana d'an murmushi had'e da lek'en fuskansa da ya kawar da ita gefe... Murmushin shima yayi mata,yana kad'a mata kai... ''Yeeehhhh!thnks BB na'' ''Laaa!YAYANAH taso kaga abunda muka maka'' Ta kama hannunsa tana jaa zuwa dinning,a hankali ya bita har gurin tarin warmers en ya kallah yana tab'e baki,yasan dai wannan kam sai dai ko idan y'an aiki suka yi amma ba MAMAN ba bare kuma wad'ancan sangartattun biyu... ''Nikam sis kyale ni da wannan shirman masu aikin'' ''Laaaa!YAYA fa mu mukayi,zauna kaga Allah yayi sweet sosai,kuma favourite naka mukayi'' Ta jaa masa kujeran tana turashi har sai da ya zauna,shi sam baya jin zai tab'a iya cin abincin masu aiki duk k'azamai dasu su maka wani abinci kuma mutum ya ci,k'amshin da ya ziyarceshi shi ya dakatar da shi daga maganar da yake yabi warmers en da kallo... Drink en da take tsiyayawa a cup shi yabi da kallo sai k'amshi yake,murmushi yayi mata ganin yadda take ta rawar k'afa a kansa ya juya parlor ya kallesu duk sun zuba musu ido suna jiran ganin abunda zai faru,juyowa yayi ya sake kallonta yanda take masa yasa ya k'udirce a ransa ba zai bata kunya ba,ko da zai ci ya haras da shi zai gwada... Cup en da ta cika da sob'o ta mik'a masa tana fad'in ''YAH bismillah!'' Karb'a yayi ya d'an d'osana cup en a bakinsa har da runtse ido,duk da yadda yake k'amshi bai gama tabbatarwa a ransa zaiyi dad'i ba sai da ya sha,aiko take ya shanye cup en hannunsa zuciyarsa cike da tunanin waye yayi wannan drink en haka? Cup en ya mik'a mata,zuciyansa ta lula duniyar tunani..... 《《》》 Tun bayan da ZAHRA ta bar gurin itama ko zaman ya isheta,bata wani jima ba ta bar gurin,inda ta k'ule cikin d'aki tana aikin kuka da ya zame mata abokin rayuwa duk lokacin da ta tuna MAMANTA.... Ta jima a haka kafin da k'yar ta tsaida kukan,ta hanyar d'auro alwala ta tada sallah...... *_~#TEAM KHUBRA~_* *_REAL SMASHER. 🤞🏻😘_* 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *4/ʍɑվ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* _íղɑ ʍɑԵմҡ'ɑɾ ցօժíվɑ ՏօՏɑí ʍɑՏօվɑ,Տɑҡ'օղҡմ ɑ ҡմӀӀմʍ վɑղɑ ɾíՏҡɑԵɑ,ղɑ ցօժҽ ɑժժմ'օ'íղҡմ,ɑӀӀɑհ վɑ ҍɑɾ ҡ'ɑմղɑ.._ *ɾҽɑӀӀվ ӀմѵՏ մ ʍվ ԹҽԹՏ..💓💓* *~________________________~* _Tabbas ba dan bak'ar addu'ah babu kyaubaa da babu abunda zai hanani kwana yi miki addu'ar da sai kin gwammace baki zo duniyarba, amma kam tabbas mun barki da Allah shi kad'ai zai nuna miki ishara, Allah ya isar mana....._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *2⃣1⃣* *T*un kafin ta idar ko bacci ya fara fisganta,da sauri tayi sallama da rarrafe ta haye kan katifan ko addu'anma idanunta a kulle suke kan bacci haka tayi addu'an kwanciya bacci,ko ninke abun sallan bata yiba bare hijab en da ta cillar a k'asa... Cikakken mintuna uku sun yi mata yawa take bacci mai nauyi ya d'auketa...... 《《》》 Zuba masa ta sake yi,shi ko sai dad'a kafa kai yake yana shanyewa a haka har sai da ya sha rabin jug en,sam bai sani ba yana can duniyar tunani,dariyan da ta saka ne ya dawo da shi diniyarsa yana mai binta da kallo,hannunsa ya sake sauke idanunsa har lokacin cup en na mak'ale a hannunsa,d'an murmushi yayi yana shafa kansa... ''YAH me zan sa maka?'' Tambayanta ya katse mishi tunani ''Anything ma sis'' Murmurshi tayi tana jin dad'in yadda yake nuna kulawa kan komai da take yi... Wani warmer ta bud'e take ko ta zaro faifan sinasir,aiko yana gani ya hau murmushi coz yana sonsa sosai MAMA ce dai da yake ba wani iya girkin gargajiya tayi ba,ko da yake na zamaninma dai da sauk'i,(auu kada ta jiyo ni) ☺....... Ai ko take ya dakatar da ita ta hanyar fad'in ''Sisnah bar shi haka ai kin gamamin komai tunda kikamin favourite nawa,sauran ki kyauta idan na gama abunda nake'' Sosai ya dage yaci sinasir en da miyan agusi,sukam su ASHNA suna cikin parlor duk abunda ke faruwa tsakanin ZAHRA da YAYAN NASU sun zuba ido ne suga ya zasu k'arke shi da ba cin abincin masu aiki yake ba,sai dai kuma kash abunda suka zata bai faruba,duk kuwa da sun san suna shiri sosai da ZAHRA a kan abuncin masu aiki komai zai iya faruwa hatta kuwa ita kanta ZAHRAN,sosai ya basu mamaki,sai da yaji uwa bazai iya tashiba sannan ya hak'ura tas ya shanye sob'on,fuskansa d'auke da fara'a ya kalli ZAHRA yana fad'in ''Thnks Lil sis'' Murmushin itama ta mayar masa kafin suka koma parlor da yake tsit uwa ba mutane... Tabbatarwa da sukayi ya gama MAMA da muk'arrabanta suka dira a dinning en,har suna rige² gurin bud'e warmer en sinasir aiko dai² lokacin ya juya ya kallesu a hankali ya furta ''Lil sis maza ki adanamin sinasir ennan,coz da safe shi nake son ci'' ''Laaaaa!BB ya maka ne?'' Kai ya kad'a mata ''To ai muna da garin,da safen sai ayi maka sabo'' Bai ce komaiba zuwa wani lokaci kuma ya soma tambayanta ''Lilly a ina kika koyi girki ne?'' ''Laaaa!BB bafa ni nayiba,kawai dai ina taimaka mata,kuma ina ganin yadda take yi'' ''Kin kyauta sosai da kike koyo kin fi wancan sakarkarun'' Har yayi shiru kuma sai ya tuna maganarta da take cewa ''ba ita tayi ba'',kenan waye yayi? Yama kansa tambayan,aiko take ya d'ago yana kallonta ''Waye ne yayi lil sis?'' ''Uhmmm YAYA wata ce'' ''Aiko ta burgeni sosai da ta iya kalolin abunda nake so'' ''Da gaske YAH?'' Kai ya sake kad'a mata,aiko sai murna take tace ''Ai kam kama tunamin ta ce zata zo maka sannu da dawowa,amma har yanzun shiru'' Shi dai yana saurarenta sai firan take masa tana ta bashi labarin irin kirkinta sai dai har lokacin bata ambaci sunanta ba,tunda suke bata tab'a masa maganar wani ba sai yau,har ta soma jin bacci,k'arshe kam sallama sukama sauran har bakin k'ofan d'akinta ya rakara ya mata sai da safe,sannan ya wuce nasa room en.... Bai jima da shigaba ko shima yabi lafiyan bed dama gajiyan bawai ya gama sakinsa bane aiko bacci ya d'aukesa babu b'ata lokaci...... 《《》》 Duk duniyar a yau kam haushin kowa take ji,haka ta wuni ranan takaici duk ya cika mata zuciya.... Ko da dare yayi,tana shiga d'akinta ta ganshi zaune kan gadonta ita kam ma har tsoro abun ya bata dan kam ta san bata bar kowa ciki ba,taya zata ga mutum kuma zaune yanzun... Har ta juya zata kwasa da gudu, ya dakatar da ita ta hanyar nuni zuwa k'afafunta,take ko tajita uwa wacce aka d'aure,bakinta har rawa yake gurin magana,sai dai ta kasa furta ko (A).... Ta kowa yayi har gabanta ganinsa ne yasa jikinta ya dad'a yin sanyi,danko tasan zasu maimaita jiya ne.... Bata gama tunanitanba ya shek'e da wata irin dariya da ta cika d'akin ita kam jikinta duk ya saki,daga nan kuma labari ya chanza salo...... Kamar waccan ranar ba shi ya k'yaleta ba sai gabanin b'illowar alfijr...... Haka ya tafi ya barta duk bak'in ciki ya dabaibayeta,tana tunane tunanenta bacci yayi gaba d ita.... 《《》》 Tun da ta farka ta d'auro alwala tana kan abun sallah har aka kira sallah,sannan ta saurara tayi sallan subh,tana zaune tana lazimi,garin ya soma haske ci gaba tayi har gari ya gama yin haske tukun ta mik'e.. Wanka tayi ta shirya cikin dogon riga cikin irin kayan da ZAHRA ke bata,ta zura hijab en sallahnta ta fice.... Karafniyarta a kitchen ZAHRA ta jiyo,aiko itama ta kamo hanya ta fito,after sun gaisa ZAHRA ta kalli KHUBRA ta fad'in ''Shi ne kika cemun zaki zo amma naji ki shiru ko?'' 'Dan murmushi tayi ba tare da ta ce komai ba ta ci gaba da aikinta ''Aiko sis ban baki labari ba,wollah jiya BB ya ban mamaki,kin san ba abincin kowa yake ciba,kuma wallahi ciki har da na MAMA,in fad'a miki sob'on da kika had'a fa tas ya shanye bai rage komai ba'' 'Yar dariyanta ta sake yi,tana shirin d'ora gyad'anta a wuta dan yau kam kunun gyad'a ta tashi da niyyan yi..... ''Laaaaa!sis ban fad'a miki ba,wallahi BB cewa yayi na ajiye masa sinasir en jiya ni kuma nace mishi ya bari a yi masa wani da safe'' Ta tak'aice maganar tana kallon KHUBRA tana kuma sauraron taji me za tace,dafe kanta KHUBRA tayi kafin ta kalleta ''Kin san kuwa sauran garin kenan jiya mukayi amfani da shi?'' Zaro ido ZAHRA tayi tana dafe kai ''Wayyo Allah na,yanzun gashi na bari sun ciye masa,da na sani na adana masa,amma yanzun mene abunyi sis?'' Fuskanta uwa za tayi kuka take kallon KHUBRA,d'an murmushi tayi na k'arfafa mata guiwa ''Hak'uri za ki bashi,amma kam baki kyauta ba'' ''Wallahi sis sam na manta sauran garin kenan,shi yasa na ce za ayi masa wani'' ''Shi kenan ki bar damuwa,yanzun kawai muyi FUNKASO in yaso sai ki kai masa shi,ki kumayi masa bayanin abunda ya faru,in ba jaka ba zai d'aukeki a mak'aryaciya idan har kika jira ya fara tambaya'' ''To sis na gode sosai'' Jikinta a salub'e haka suka ci gaba da aikinsu'' Juya baya KHUBRA tayi ta ci gaba da aikin kwab'in funkasonta.... Tun da ya tashi wanka kad'ai yayi ya zura jallabiya milk colour,silifas en wanka ya zura ya fito,a hankali yake tafiya ko wata macen baza ta gaya masa tafiya a nutse ba... K'amshin girkin ya biyo,har kusa da kitchen en,nan ne ya soma jin magana k'asa²,a bakin k'ofan ya tsaya yana kallon yadda suka zage suna aiki,ya dai ga ZAHRA kam da yake tana gefe sai surutu take zubawa... Ita ko d'ayar sam baya iya hango fuskanta,saboda haka bai wani damu da sanin wace ba... Juywa yayi zai bar gurin dai² ZAHRA ta d'an waigo ai ko ta ganshi,da suri ta biyo shi parlor tana fad'in ''YAYANAH barka da safiya'' Fuskarsa da y'ar fara'a ya kalleta yana amsata,nan kuma tayi shiru kafin cikin d'an tsoro² ta ce ''YAYANAH idan na fad'a maka wata magana baza kaji haushi ba?'' ''No princess bazan ji ba,ai bakya laifi a gurina'' ''Ammmm!dama ko YAH garin shinkafan da za muyi maka sinasir ne ya k'are,na manta jiya nace maka akwai,amma dan Allah kayi hak'uri kaji'' ''Nooo!Princess kar ki damu,babu komai maza jeki ku ci gaba da aikin'' ''To YAYANAH na gode sosai'' Murmushi ya mata kafin da d'an gudunta ta bar gurin ta nufi kitchen en..... Tana shiga ta tarar da KHUBRA har ta gama kwab'in,tana juya kununta da ta dama,da y'ar murnanta ta juyo ta kalleta ''Wato ko sis ina fad'a miki kin san baimin fad'a ba kuma Allah bai damu ba'' ''Ai na fad'a miki dama gara da kika fad'a masa yanzun kafin ya tambayeki,da shi ya riga tambaya Allah sai ya ji haushinki'' ''Ai kuwa dai wallahi yanzun dad'i nake ji da na fad'a masa kuma bai nunamin damuwa ba'' Ita kam sai murmushi take tana aikinta,haka har ta k'are komai tana k'ok'arin soma suyan funkason,mutiyar tana gefe zaune kan stool tana mata fira... Sai da suka gama gyara komai na kitchen en kafin KHUBRA ta zari hijab enta dake kan k'ofa inda ta sak'ale shi ''Yawwa sis muje ku gaisa da BB kinga sai ki masa barka da dawowa tunda jiya baki zo ba'' Tana gama fad'in hakan ta hau jaan hannun KHUBRA,ita kam kanta ta saukar k'asa a haka suka fita cikin parlorn,suna tafiya duk jinta take wani iri uwa wacce aka yiwa duka,sai dad'a sinne kai take yi...... 《《》》 Tun bayan fitar 'DAN LADI take nan kwance duk idanunta sun gagara komawa ainihin kalarsu... Haka ta yini ita kad'ai a cikin gidan sam ta kasa tab'uka komai,tana tsaka da tunanin mafita Ogan d'an ladi ya fad'o gidan Mad'aurin............. a hannunsa ya shigo d'akin,ko sallama babu ya k'arasa har gaban MA'U dake kwance idanunta rufe,sam ta kasa bud'e idanunta bare ta ga waye ya shigo,dan ba buk'atarta kenan ba.... Jin mutum tayi kawai yana juyata,cikin kasala ta d'an soma bud'e idanuntan a hankali hoton face ensa suka yi arba da k'wayar idanta,take ta maidasu ta rufe,aiko nan take suka fad'a harka wacce bata da tsayayyen lokacin da za su daina sai lokacin da suka yi ra'ayi...... Sam a yanzu MA'U ta manta da babin wata halitta mai kama da KHUBRA wacce iya tsawon watanni hud'u (4) kenan bata sake bi ta kan kud'in aikin KHUBRAN ba,dan ko itama tana kan samun nata na k'ashin kanta,dan ko dama can fatara ce tasa take damuwa da samun su,to yanzun nata k'ofofin samun sun bud'e shi yasa sam ta manta da ita..... 《《》》 A tsakiyar parlorn suka ja burki sai dai babu kowa cikin parlorn,waige² ZAHRA take yi amma tabbas idanunta ba k'arya suke mata ba baya nan.. Har lokacin ko idanun KHUBRA na k'asa bata d'agoba bare tasan halin da ake ciki... Zaunar da ita ZAHRA tayi tana fad'in ''Sis zauna nan ina dawowa,barin kirashi ku gaisa'' Tana gama fad'a tayi hanyan corridor da zai sada ta da bedroom ensa... A hankali ta d'ago kanta ta kalli cikin parlorn sai da ta tabbatar ZAHRA tayi nisa sannan ta mik'e cikin sand'a ta fice daga parlorn,ganinta a waje tayiwa Allah godiya,take ko ta kwasa a guje,ba ita ta dakata ba sai da ta tsinci kanta cikin d'akinta sannan ta mai da k'ofan tayi locking nata,ta shiga mai da uwa wacce ta shiga gasar there ta duniya............ *_~TEAM KHUBRA~_* *_REAL SMASHER._* 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *Viawattpad@realsmasher01.* *©®2018* *6/ʍɑվ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *հҽհҽհҽհҽհҽ!!* _ժɑɾíվɑɾ ɾɑíղíղ աɑվօ ҡҽղɑղ,ցɑ աɑղժɑ վɑ ԵՏɑɾցմ..._ _íղɑ ʍíҡ'օ ցɑíՏմաɑ վ'ɑղ ɑʍɑղɑ ʍմԵaղҽղɑ,abօҡan tsoҡana,sarɑkan riҡici.աղղ Տհí ղҽ Եɑҡҽղҡմ._ *DURLING SIS MY HUBBEEY* *MY LEEMA* *AUNTY MAIMOUNATH (O.G)* *AUNTY MEELAT* *HASEENA OGANNIYA ND D REST...* _Aɾɑժմ íղɑ վíղҡմ íɾíղ ҍɑՀɑ ɑ ɾɑҍմҍɑ ҽղղɑղ AӀӀɑհ վɑ ҍɑɾ Հմʍմղcí ժɑ ҡ'ɑմղɑ,վɑ ҡմʍɑ ҡɑɾҽʍմ Տհɑɾɾíղ ʍɑՏմ Տհɑɾɾí..._ *~________________________~* _íղɑ ʍɑԵմҡ'ɑɾ ցօժíվɑ ՏօՏɑí ժմɾӀíղց ҍɾօԵհҽɾ ժɑ ցվɑɾɑղ ժɑ ҡɑʍíղ,AӀӀɑհ վɑ ҍɑɾ Հմʍմղcí.._ _ցɑíՏմաɑ ժɑ faԵan ɑӀҡհɑíɾí ցɑɾҽҡɑ *Տɑժҽҽզ ɑʍíղմ վɑհվɑ (ԹíӀօԵ)* աօӀӀɑհ ɑղɑ ʍմցմղ Եɑɾҽ ʍվ ҍɾօ.._ *~________________________~* _Aradu sai dai idon mak'iya ya fad'o k'asa,ka sha gabansu,ka wuce gaban kwatance duk mak'iyinka sai dai ya sadda kansa k'asa idan akace ga kanan,OUR SURUKI ka wuce da saninsu,yara baza su jaa da kaiba dan ko kafi k'arfinsu......Yeahhhh kai kad'ai nake nufi *(HASSAN ATK)* Allah ya bar zumunci ya maka nisan kwana mai amfani,mu da kai mutu ka raba (takalmin kaza) k'aryar mak'iya su shiga tsakaninmu,na jinjina maka OUR SURUKI,Allah jaa da ranka...._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *2⃣2⃣* *Nɑվí ʍíՏԵɑҡҽ աɑյҽղ sunan ZUHRA íղɑ ʍɑí ժɑՏհí ZAHRA, Տօ ZUHRA ղҽ վղՀղ ҍɑ ZAHRA ҍɑ,ɑʍíղ ɑƒմաɑ,ԵհղҡՏ ҍɾօԵհҽɾ ƒօɾ cօɾɾҽcԵíօղ..* *C*hest enta ta dafe saboda yadda take jin zuciyanta na skipping uwa zai faso ya fito,duk ta gama tsorata kanta,da k'yar ta ja k'afafunta ta zauna bakin katifanta,hijab en dake jikinta ta cire duk ta had'a gumi uwa wacce tayi gudun kilometer's.... Kumatunta ta tallafe tana faman mai da numfashi,a fili ta shiga magana ita d'aya ''Wai Allah ya soni,ai gara da na gudu tun basu zo sun tarar da ni ba'' Can kuma ta sa dariya uwa tab'ab'b'iya,kun san KHUBRA dama gwana ce gurin dariyar mugunta tun bama akan MA'U ba,ita kam haka halinta yake..... 《《》》 Ko da ZUHRA ta bi corridor en direct bedroom en sa ta nufa,handle en k'ofan ta shiga k'ok'arin murd'awa amma a rufe yake,knocking ta shiga yi amma shiru,hakan yasa ta juya ta koma parlor gurin KHUBRA... Sai dai me tana zuwa taga wayam ba KHUBRA babu dalilinta,kitchen ta koma ta gani ko tana can aiko tana zuwa nan ma fayau bata nan.... Fitowa tayi ta nufi hanyan side enta,sai da ta biya ta guarding coz tasan nan ne gurin zamansu ganin bata nan ta kama hanyan d'akinta zuciyanta fal mamakin KHUBRAN ''Ko mene yasa ta tafi kuma ohooo?'' Ita kad'ai tana tafiya tana surutu har ta k'araso k'ofan d'akin...... A kulle ta ga k'ofan har zata koma,sai kuma ta juyo a bakin k'ofan ta tsaya ta d'ora hannunta akan k'ofan ta shiga knocking.... KHUBRA dake zaune ta tallafe kumatu da hannayenta duka biyu tana faman sana'ar tunani taji ana knocking,da uwa bara ta bud'e ba,sai kuma ta tashi tana bud'ewa sukayi arba da ZUHRA,kallonta kad'ai tayi kafin ta shigo ciki.... Kanta a k'asa ta k'i yarda su had'a ido da ZUHRA,ita kuma ta kasa magana tun da ta shigo sai bin KHUBRAN take da kallo,da k'yar dai ZUHRA tayi k'ok'arin dakatar da shirun nasu... ''To meye na wani guduwa,kina gani ma na je k'ofan nasa anyi locking enta ta ciki'' Cike da jin haushi take yin maganar,sai cuno baki take yi gaba... Ajiyan heart KHUBRA tayi nan ko ta soma kame²n abunda za tace,ZUHRAN ta katseta da fad'in ''Maybe ko akwai abunda yake amma gaskiya BB baya kulle k'ofa hakanan'' Fira suka soma kamar kowane lokaci sunata dariya abunsu,tuni sukayi fatali da wancan zancen... Suna tsaka da dariyan ne HANEEF ya fad'o d'akin ba tare da Sallama ba yana haki ya hau fad'in ''YAH ZUHRA wai ki zo inji YAYA'' ''Ok!muje gani nan zuwa yanzun'' Ficewa yayi a guje,tun kafin ta juyo KHUBRA tayi tsalle tana nufan hanyan toilet,juyowa tayi tana kallonta ''Ina kuma zaki yanzu,ki zo muje sai mu dawo tare'' ''Eyyahhh!sis yi gaba zan biyoki kinga wanka zanyi,Allah yau zafi nake ji'' Duk ta wani marairaice fuska uwa za tayi kuka take maganar Y'ar dariya ZUHRA tayi kafin ta mik'e tana tafiya ''Ke dai kya fad'i gaskiya dan kam tsaf na harbo jirginki,YAYANAH ne baki son gaisawa da shi,ai shi kenan ba komai dama duniya ta gaji haka'' Tana gama fad'in maganar tata tayi waje da d'an gudunta ta bar gurin... Kafad'a KHUBRA ta d'age sama,alaman ko a jikina sannan ta shige toilet en..... Tana shiga parlorn ta tarar da shi ya shirya tsaf cikin wasu k'ananan kaya sun matuk'ar amsar fatarsa,da sauri ta isa kusa da shi ta zauna ''BB nah gani'' ''Waye yaje yanamin knocking k'ofa d'azun?'' ''Laaaa! BB nice fa'' ''Ok!nayi tunanin ko wad'ancan fitsararrun ne'' ''Uhmmm!a'a,dama k'awata na kawo maka ku gaisa,wacce na fad'a maka ennan to ita cefa,kuma ko da baka nan tana yi maka add'uah idan ina bata labarinka'' Murmushi kad'ai ya mata kafin ya furta ''Ok na gode sosai'' ''Yawwa BB ga breakfast enka can,amma koh sai ka canki mene mukayi'' ''Uhmmm!ZUHRA Allah ya shiryamin ke kin cika shirme,muje ni kam'' Har sun nufi dinning area en wayansa ya fara ring da yake cikin parlor ya barosu,ZUHRA ce ta koma ta d'auko masa,aiko ta mik'o masa dai² time en wayan ya yanke... Yana shirin dubawa wani kiran ya sake shigowa,d'an murmushi yayi kafin ya dai²ta fuskansa uwa ba shi yayi murmushinba,yana d'aukan kiran.... ''Hello!yane da wannan safiyan zaka kirani?'' Banji me aka fad'a daga d'ayan side enba,kawai dai naji ya furta ''Ok!sai ka shigo en'' Tuni yayi hanging kiran sai kace shi ya kira... 'Dan juyawa yayi ya kalli ZUHRA da take tsaye har lokacin tana raba eyes uwa mara gaskiya ''UHUMMM!ke kuma tsaiwan mene kike haka ?'' Murya k'asa² yake maganar kamar baison magana,ko da yake na fuskanci haka d'abi'arsace.... Kujera ta janyo tana daga tsaye ta shiga serving ensa,yana can yana pressing phone baima san me take ba har ta kammala,ta zauna tana k'ok'arin soma cin nata,ya d'ago yana bin plates en da kallo.... Wani arnen smile ya saki lokacin da yayi arba da plate nasa,ko uffan bai ce ba sai da ya tabbatar ya k'oshi,tukun ya kalleta.... ''Kai sis gaskiya ko wace ce tayi girkin nan ta burgeni coz ta gama sanin favourite nawa'' ''Aaaaaa!BB mun iya dai'' ''A'a fa ita dai ke ai aikin surutu kad'ai kike yi,bayan na gani da idona'' ''Uhmmm!kawai dai BB santi kake yi,laaaaa!na manta k'awar nan tawace fa da na gama baka labari yanzun'' ''Uhmmm!wai kam Sis a ina take ne,da har ta iya baro nasu gidan da safiyar nan tazo taya ki aiki?'' Sai da tayi dariya son ranta sannan ta iya magana ''BB a nan gidanfa take da zama'' Da sauri ya kalleta,coz bai gane inda maganarta ta dosa ba ''Ehh pha!a nan gidan take'' Nan ta kwashe komai na alak'arta da KHUBRAN ta sanar masa... Ajiyan heart yayi,a ransa ko fad'i yake ''Tabbbb gaskiya tunda nake ban tab'a ganin housemaid kamar ta ba,gaskiya wannan ta daban ce'' ''BB barin je gurinta na barota ita kad'ai'' Tun kafin ya bata amsa har ta fice daga parlorn,bayanta yabi da kallo yana jinjina al'amarin a zuciyansa,ko me ya tuna ya d'age kafad'ansa yana fad'in ''To ni mene ma na damuwa,da zan tsaya tunani''..... Dafe kai yayi yana fad'in ''Ohh!God na manta ban sanarma Sisnah ba zanyi bak'o'' Dai² lokacin ASHNA ta shigo parlorn taci wasu k'ananan kaya duk sun d'ameta,wani kallo ya mata cike da harara,take ko zuciyarsa ta dad'a tunziro shi aiko ya hauta da fad'a ''Ke don kin raina mutane,uban waye ya sa kike irin wannan shigan a gidan nan,saboda kinga bana nan koh?to wallahi ki maida hankalinki jikinki in ba haka ba ina mai b'allaki,wawuya kawai kina girma kina dad'a cin k'asa,Allah ya sa na k'ara ganinki da irin wad'annan kayan kiga yadda zanyi da ke...........Kin b'ace min anan ko sai jikinki ya gaya miki?'' Yi yayi uwa zai tashi,aiko ba shiri ASHNAR ta kwasa a guje sai bedroom nata,bata sake fitowa ba,ta ci gaba da zama ciki.... FATAHIYYA ce ta fito idonta uwa na aljanu duk ya sha hauka,shi da ya kalletama dariya taso bashi,amma ya doje yak'i yi ''Ke je ki kiramun AUNTYNKI'' ''YAYA wacce AUNTYN?'' kanta a k'asa uwa munafuka tayi tambayar,d'agowa yayi ya kalleta ''Wacce kika san ina nufi'' Ya bata amsa a d'an hasale,ba shiri ta fice dan tasan bata cikin gidan kam,d'akin KHUBRA ta nufa direct,sun rashe saman katifa sunata faman dariya ta shigo ,ko kallon arzik'i bata musuba su duka ta furta ''Ki zo inji YAYA'' Daga haka ta juya,ba tare da ta jira amsar ta ba... "To barin je inji me kuma BB zai ce yanzun,yaukam ina shan kira gurinsa'' Kai KHUBRA ta sunkuyar k'asa dan yanzun kam bata san me zata yiba wanda zai ceceta don ma kada ZUHRA tace ta zo su tafi tare..... Cikin ikon Allah da sauri ZUHRAN ta fita bata ko neme ta kan su tafi tare ba.... Godiya tayiwa Allah da hakan ta faru,aiko ta d'auko littafinta na da take rubutu cikinsa,nan ta shiga (bahas) kan girkin da za tayi yau..... ZUHRA ce ta shigo tana tsalle,a hankali ta janye littafin daga kan fuskanta tana kallonta... ''Maza ta so sis,yau akwai aiki a gabanmu,dan BB ya sanarmin zaiyi bak'o yau kam,so yanzun ya kamata musan abun yi'' ''Tohh!muje kada mu b'ata lokaci'' Da sauri ta zari hijab enta,ita kuma ZUHRA ta kama hannunta suka fice suna rufe d'akin.... A kitchen suka yada zango,nan kuwa suka kachame a kitchen en sai aiki suke suna hirarsu duk da mafi yawanci surutun na ZUHRA ne.... Misalin k'arfe 1:30 suka jiyo maganansu k'asa²,da yake lokacin sun kusa kammalawa,aiko nan suka dad'a bada himma...... Sun d'an jima da shigowa sannan HAJIYA MURJA da muk'arrabanta suka fito,ASHNA tana ganin bak'on aka chanza tafiya sai kwarkwasa take,aiko FATAHIYYA ma na ganin haka itama ta shiga gyara tafiyarta,ko wajen magana ma sai ta sirance murya tana gaida shi..... A hankali ya d'ago yana kallonsu,gaye ajin farko a kyau,iya kwaliyya,tsafta,gayu,ya had'e cikin wasu k'ananan kaya sam banyi tunanin yana jin yaren da suka masa ba,take ko ya musu wani kallon k'asan ido yana amsawa da k'yar.... Duk bidirin da ake babu ZUHRA a gurin,suna can suna fama a kitchen.... Sun kammala komai setting teble kad'ai ya rage musu,aiko nan ZUHRA ta hau tsokanar KHUBRA kan sai dai ta fita da kayan,dan ta san da wuya ta fitan,coz ta fuskanci tun da YAYAN nata ya dawo bata tab'a gigin barin sun had'uba,ko mene hakan ke nufi ohhoo???.... Da kyar ZUHRAN ta soma kwasar kayan tana fita da shi dan tasan kam KHUBRAN ba zataba,tun da ta jiyo muryansu ASHNA da MAMA.... Drink en da take had'awa ne kad'ai ya rage basu fita da shiba,jin parlorn shiru yasa KHUBRAN zura hijab enta ta nufi hanyan fita a tunaninta tana ajiyewa sai tayi waje ba tare da sun had'u da kowa ba.... Sam bata yi tsammaniba,kanta a k'asa take tafiya har dinning arean,k'asa² taji magana wanda yasa ta d'ago a d'an tsorace,suna zaune dukansu a gurin wata harara HAJIYAN ta aiko mata da yasa ta dad'a sadda kanta k'asa still tayi a gurin har sai da HAJIYAN tayi magana.... ''Me kike jira a nan gurin,kina b'atawa mutane lokaci'' A hankali ta ci gaba da tafiya har dinning en,sai dad'a janyo hijab enta take tana rufe fuskanta.... Ajiyewa tayi zata bar gurin,HAJIYAN ta sake dakatar da ita ''Waye zaiyi servings da kike k'ok'arin barin gurin?'' Dawowa tayi jikinta a sanyaye jikinta sai rawa yake,plate na farko da tayi serving ta mik'a gaban HAJIYAN saboda tafi kusa da HAJIYAN... Duk su biyun sun tsaya kallonta yanda ta wani k'udundune kanta cikin hijab... Shi dai BB tab'e baki yayi yana pressing wayansa,shima dai abokin nasa bakin ya tab'e ya koma yana duba wrist watch en sa.... Ta side ensu ta zagayo ta shiga serving nasu,tsaf ta kammala ta janyo cup's ta zuba drink ciki.... Hannu ya mik'a zai d'auka,ita kuma tana k'ok'arin ajiye d'ayan na hannunta,hannunsa ne ya tankwab'e nata aiko take suka zube masa a jiki,cikin sauri ya furta ''Ya salaam!'' Da saurin itama ta soma bashi hak'uri,still hijab enta na a yanda ta sashi,sweetest voice nata shi ya dokesu su biyun suka bita da kallo,ko kafin suyi aune tuni suka tsinkayo muryan HAJIYA MURJA tana fad'a cikin kaushin murya.... ''Amma wannan kwoi sha³ kin rufe fuska dama uwa wata munafuka taya zaki san me kike?'' Dukkansu basu ji dad'in abunda tayi ba,hayaniyan da ZUHRA ta jiyo ne yasa ta fito da sauri daga kitchen,lokacin da ta k'araso gurin a lokacin ita kuma KHUBRA ta juya tana kuka ta nufi hanyan fita ko gabanta bata iya gani sosai.... *KHUBRA!!!* ZUHRA ta shiga kiranta da d'an k'arfi,a tare suka d'ago suna masu bin hanyan da tabi da kallo,basu ga kowa ba lokacin ne kuma ZUHRAN ta bita,hakan ya tabbatar musu da sunan wacce ta fita kenan...... Har suka gama babu wanda ya sake magana,sun d'an jima suna hira kafin ya ta shi tafiya.... BB ne ya kira HAJIYANSU,sallama yayi mata yana fad'in zai tafi sai an kwana biyu kuma..... ''Toh *KHALEEL* ka gaida gida da HAJIYAN ka dan Allah,kace mata zan shigo cikin wani satin'' Amsa mata yayi,suka nufi hanyan fita..... 《《》》 Tun da ta fita bata tsaya ko inaba sai guarding a can taja breke aiko take ZUHRA ta k'araso nan ta rungumeta tana bata hak'uri,har tayi shiru,nan suka ci gaba da firansu.... Dariya KHUBRA take kan labarin da ZUHRA ke bata,aiko me za tayi banda dariya,nan ko ZUHRAN ta shiga tsokanarta "Mai kuka tana dariya........ai mata d'an kwad'on daddawa",guje² suka hau yi cikin guarding en,sam ta kasa kamata haka sukayi ta yi har sai da suka fito waje,kwata² basu kula da fitowan mutum ba sai gudun suke lokacin KHUBRA ta zo giftawa sukayi karo,take gefen hijab enta tayi ta tafi tana shirin fad'uwa................. *_~TEAM KHUBRA~_* *_REAL SMASHER._*🤞🏻😘 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *7/ʍɑվ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~________________________~* _Gaisuwa tare da fatan alkhairi gareku y'an uwa,masoya *KHADIJA IBRAHIM YUSUF (KHADEEY)* da bestei en ki *NUSAIBA IBRAHIM ISSAH (NUSEEY)* ,Allah ya k'ara muku k'aunar juna,Allah kuma ya k'arawa sis *KHADEEY* lafiya mai d'orewa,tabbas *SMASHER* taga sak'onku,ina godiya wacce bata da iyaka,Y'an group en *SMASHER ND HUBBEEY* suna godiya,Allah ya bar zumunci.._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *2⃣3⃣* *J*ikinta gaba d'aya banda rawa babu abunda yake,yayin da idanuwanta ke a kulle coz ta gama saddak'arwa sai ta sha k'asa..... Ita kanta ZUHRA sai da ta tsorata bama kamar kallon da BB yake watso mata,sukam sun k'ame uwa poster,shi bai saketa ba,ita kuma bata yi k'ok'arin kwacewaba,jin abu ya tare ta yasa ta soma bud'e ido a hankali..... KHALEEL dake gefensa time en sun jero ya juya ya kalli BB dake rik'e da ita....... Gaba d'aya idanunsa na kanta,coz babu abunda ya b'uyan masa na daga fuskanta,kallonta suke like no other,wanda yanda take bud'e idanun tama ya bada wani style na daban.... Arba da tayi da fuskan mutum shi yasa tayi k'ok'arin mik'ewa daga rik'on da yayi mata,sassauta mata rik'on yayi ta mik'e da kanta.... Tafiya suka ci gaba da yi suna masu waiwayowa dukansu suka sake binta da kallo,kowa da abunda yake sak'awa a ransa.... BB ne ya fara janye eyes ensa daga kanta,zuciyarsa fal tunanin ''Ina Sis ta samo wannan shuwa-arab en?'' Dan kam shi dai ya tabbatar sai an tona kafin a samo mai kyau irin nata,dan shi kam a cewarsa wannan batayi ruwa da nan ba sai dai ko UNITED ARAB..... Shi ko KHALEEL zuciyarsa taff take da tambayoyi,wanda yake jin ba zai iya barin ya tafi da su ba tare da ya amayarba... BB ya kallah dake gefensa yana fad'in *KHALEED!* ''yaushe kukayi bak'uwa,dama kuna da y'an uwa wata k'asar ban tab'ajin ko a labariba?'' Rasa abun cewa *KHALEED* en yayi wato *(BBN ZUHRA)* ,yana can kogin tunani,bai sanma *KHALEEL* na masa magana ba,har sai da ya dafa shi... ''Wannan k'anwace a gurinka ba?'' 'Dan murmushi yayi yana nodding kansa..... Rasa abun fad'a KHALEEL en yayi,kawai sai ya hak'ura yayi shiru,amma a zuciyarsa yana godiya ga Allah da KHUBRAN ta kasance k'anwa a gurinsa kuma y'ar gidan,duk da dai bai san ya alak'arsu take ba.... Haka suka yi sallama ya shige motor ensa ya fice daga gidan suna waving wa junansu.... Tun da ta samu ya saketa,ta sunkuyar da kai k'asa ganin irin kallon da suke mata,bata sake d'agowaba har sai da suka bar wajen tukun,shima tsokanarta ZUHRA take shi ne dalilin da yasa ta d'ago,sai da ta gama k'arewa gurin kallo tukun suka sake d'orawa daga inda suka tsaya....... ''Yarinya kinga kallon da mazaje suke miki kuwa,Allah na fad'a miki kina da kyau kink'i yarda,soon zaki tabbatar'' Tana gama fad'a ta shek'a a guje,nan ko KHUBRAN ta bita (niko cewa nayi baki daddaraba kenan)..... Dan kansu suka zube cikin guarding suna dariya,ba kuma su fasa tsokanar junanba..... Tun da ya samu KHALEEL ya tafi,ya juyo kallon sides na gidan ya shiga yi ko zai sake arba da fuskanta,amma kamar aljana,haka yaita kalle² a gidan ko mai kama da ita bai gani ta b'illoba bare itan...... Hak'ura yayi ya shige bedroom ensa,kwanciya yayi fuskanta ta shiga yi masa gizo,shi kad'ai sai dai yayi murmushi,haka yaita juyi saman bed (Uhmnmm!BB ayi a hankali kar a fad'o k'asafa inji HUBBEEY☺)...... 《《》》 Driving yake amma tunani duk ya dame shi,shi kad'ai yake magana a motern ''Gaskiya zan sanarma UMMI gara ta nemomin mafita,tun kafin wani ya rigani gara tayi magana'' Wannan tunanin da yayi shi ya bashi nutsuwa da murnansa ya isa gida...... Ko bari ya isa perking lot baiba a haraban gidan ya percker,da d'an saurinsa ya fito ya nufi cikin gidan.... Sai da ya gama bulayinsa a parlor zuwa kitchen amma baiga UMMIN nasa ba,d'akinta ya nufa direct,aiko nan ya tarar da ita tana ta duba closet enta kayan ciki duk ta fiddo shi... Sallama yayi mata,jin maganar KHALEEL en ne yasa ta juyo da murmushi a fuskarta take kallonsa ''A'a SON har ka dawo?'' Kansa ya d'an shafa yana murmushin shima ''Ehh wollah na dawo,duk suna gaishe kima'' ''Aiko ina amsawa,ka baro su lafiya?'' ''Lafiya k'alau'' Har yayi shiru kuma,can dai ya ga hakan ba zai fishshe shi ba,aiko tuni ya bud'e baki ''Ammmm!UMMI dama wata magana nazo muyi,amma na ga kina aiki'' ''Wace magana ce SON?'' Nan kuma ya tsaya kame²,hakan da yake yi ne yasa ta bar abunda take,kusa da shi ta dawo ta zauna tana fuskantarsa ''Ka ce magana kuma kayi shiru,akwai abunda yake damunka ne?'' K'eyansa ya sosa kafin ya bud'e baki,uwa wanda maganarma take masa wahala ''UMMI dama fa''...... Sai kuma yayi shiru,kallonsa ta tsaya yi ''Yau naga ikon Allah,SON yau kuma kunyata kake jine ko me?'' ''No UMMI kawai dai ban san mesa na kasa fad'a ba kuma'' ''To sai ka ficemin anan tunda ba fad'a za kayi ba'' ''A'a UMMI zan fad'a wallahi'' ''Oyahh!to ina saurarenka'' Sai da ya sake yin jimmm kafin ya soma magana ''Ammm!UMMI dama fa wata yarinya na gani ne,to kuma''.... Ya sake yin shiru yana d'an sosa k'eyansa.... 'Dan murmushi tayi,tana kallonsa ''Uhmm!SON kenan wato kan maganar nan ne kake jin kunyata kuma yau?'' Kwanciya yayi kan cinyanta,yana b'oye fuska ''Ohh!ni FATIMA yau na ga abunda ya isheni mamaki'' ''Uhmmm!nifa UMMI so nake kiyi magana da ABBA tun kafin lokaci ya k'ure,kada wani ya''..... K'eyarsa ta doke,aiko ba shiri ya hantsilo k'asa yana dafe kai,da d'an murmushi ya nufi hanya zai fice ''Kai dawo nan,baka ma fad'amin a inda ka ga yarinyarba'' ''UMMI a gidansu KHALEED fa na ganta'' ''Jimin ja'iri cikin y'an gidan waye baka sani ba,da zaka bani zance a rufe'' ''No UMMI bafa cikin wad'annan fitsararrun bane,wannan daban take,Allah ko UMMI saima kin ganta'' ''Idan ba suba to wace kuma take zaune gidan?'' ''Ni dai yacemin sister ensu ce itama'' ''Ok duk koma mene ne zanji bakin HAJIYA MURJA'' ''Yawwa UMMINA na gode irin sosai ennan'' Ya fad'a yana dunk'ule hannu,kallon da ta masa ne yasa ya fice babu shiri yana dariya.... Kai ta girgiza itama tana jinjina al'amarin d'an nata..... 《《》》 Wuni guda yana cikin d'akin sallah kad'ai ke fito da shi,bayan haka ko sai dai ko idan tunani ya dame shi ya fito,haka zai ta zagaye a cikin gidan tun daga kitchen har harabar gidan amma sam ya neme ta ya rasa,shi kad'ai ya soma magana da kansa ''Anya kuwa wannan mutum ce? to amma da aljana ce ai baran ganta tare da sis ena ba,to wai nikam me yasa ma na damu da son ganinta?'' Shi kad'ai yaita fama da zancensa,sis en nasa ma ya rasa ina ta shige da ya mata tambayoyi kan yarinyar da ya gansu tare.... Hak'uri ya bama kansa ya koma parlor ya zauna,amma sam ya gagara samun sukuni,haka ya koma bedroom ya kwanta.... 《《》》 Kamar kullum yauma haka suka yi zamansu cikin guarding en,lokacin da aka kira sallan asr da gudu kamar yara sa'annin HANEEF haka suka shiga tsere zuwa bakin tap en,kafin suyi alwalanma sai da suka yita watsawa juna ruwa,da kyar suka gama suka bar gurin,a d'akinta suka yi sallah,sannan suka fito,ita KHUBRA tana haramar zuwa had'a dinner,ita kuma ZUHRA zata shirya kafin malaminsu ya k'araso,har kitchen ta raka KHUBRAN ko kafin ta tafi sai da ta taimaka mata da wasu ayyukan kafin ta mata sallama ta fice.... Aikinta taci gaba da yi ita d'aya,da yake ma ta saba da aikin,nan da nan ta kusa kammalawa...... 《《》》 Wayanta dake kuka ta kalla,duk kuwa da yadda take kusa da wayan sai da ta lek'a kafin ta d'auka daf da zata tsinke,sunan HAJIYA FATEE data gani shi yasa ta d'auka tana dariya,bayan sun gaisa HAJIYA MURJA ke sanar da UMMIN KHALEEL ''HAJIYA ina fatan sak'ona ya iskoki?'' ''Sak'o kuma na me?'' ''Na ce a sanar miki zuwa wani satin zan shigo in Allah ya kaimu'' ''Tohh Allah kuwa ya kawo ki lafiya,ammm!HAJIYA dama d'anki ne ya zo min da wani labari'' ''Labari kan me kenan?'' Cikin son jin zancen HAJIYA MURJA tayi maganar ''Ammm!dama cemin yayi ya ga yarinya a gidanki,to shi ne daga zuwansa yake sanarmin kan a nema masa izinin gurinku shi dai yana so'' ''Aarrhh!ai abu yayi kyau,amma baki bambancemin wacce daga ciki yake nufi ba ASHNA ko ZUHRA yake nufi?'' ''Gaskiya yacemin duk basu bane,amma dai ya tabbatarmin a gidanki yarinyar take'' Take ko zuciyar HAJIYA MURJA ta soma skipping,ranta duk ya b'aci da wannan maganar,daga jin wannan zancen babu alkhairi cikinsa,dan ko bata raba d'ayan biyu wannan shegiyar y'ar mai kama da aljanu yake so... Zuciyarta ta danne kafin cikin kissa ta furta ''Aiihhhooo!KHUBRA yake nufi ba...........Ai ko tabbas gidana take,sai dai wani hanzari ba guduba,gaskiya HAJIYA kiyi hak'uri da abunda za kiji yanzun.. Ita dai wannan yarinya da ake magana kanta babu wata alak'a tsakaninmu da ita face matsayinta na 'YAR AIKI,inama laifin ya duba cikin k'annen nasa ko Allah zai sa a dace'' Ita dai HAJIYA FATEE shiru tayi tana mamakin lamarin,a zuciyarta ko fad'i take ''Aiko bari SON en ya dawo,sam baza ta sab'uba(wai akace bindiga a ruwa)''........ Haka sukayi sallama,take bata jiraba ta dokawa KHALEEL waya,katsewa yayi ya kirata coz dama al'adarsa ce hakan... Bata jira tajima me zai ceba ta hau fad'in ''Maza kazo ina son ganinka'' Tana gama fad'in uzurinta ta katse kiran,sai safa da marwa take a parlor ita kad'ai.... Shigowansa parlorn ya tarar da ita a tsaye,hankalinsa har ya soma tashi ganin yanayinta... ''UMMI lafiya naga hankalinki a tashe?'' ''Dakata SON'' ta d'aga masa hannu ''Dama yarinyar da ka dameni akanta *HOUSEMAID* ce?'' ''UMMI amma fa''........... ''Bana buk'atar jin komai daga bakinka,magana d'aya zan fad'a maka ka shafe babin wannan maganar a rayuwarka,ko dai cikin k'annenka ka duba wata ko kuma ka nemo wata,amma banda wannan'' INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN Yake maimaitawa,kafin ya kalli mahaifiyar tasa ''UMMI mene laifinta,yanzun ita ba mutum bace da baza a sota ba,kuma tana da iyaye......Ni gaskiya da in auri wannan yarinyar Allah gara na k'are rayuwata babu aure''......... Kafin ya k'arasa ta wanke shi da mari tana nuna shi da hannu ''Wallahi SON baza ka kunya tani ba ASHNA ce baka so,to ka sa aranka kai da ita anyi an gama sha³''....... Dafe da kumatunsa yake kallonta,tsawon tasowansa bata tab'a masa fad'a ba,amma yau har da mari,shi kam a ransa a k'udurce shi da ASHNA sai dai kallo,me zaiyi da wannan ballagazar? Jin kalamanta na k'arshe ya tsorata,take hawaye ya shiga biyo kumatunsa,yasa hannu ya goge kallon UMMIN nasa kawai yayi ya fice.... Hawayen da ta gani a fuskarsa shi ya bata tsoro,da girmansa yake mata kuka,tabbas tasan bai tab'a ce mata ga wata mace da yake soba,lallai ko wannan yarinya duk inda ta fito ta daban ce..... Tunani duk ya addabeta,haka ta zauna duk kuma sai taji babu dad'i,tasan gaskiya ya fad'a,to wai kam ita ya za tayi ne???? Yana fita daga parlorn direct gidan ya bari dan yasan hakan kad'ai shi ne solution,idan ta nemeshi ta rasa a gidan zata sakko.... Shi kad'ai yayi wani murmushin takaici,lokaci guda kuma wata tsanar ASHNA ta diro masa,aiko nan ya lashi takobin wallahi ko me za ayi bazai tab'a aurenta ba,da haka ya d'auki hanya wanda baima san inda zai nufa ba..... 《《》》 Tsawon kwanaki uku kenan bai sake sata a idonsa ba,duk inda ya so da ya ganta kamar wacce tasha sab'ani haka suke ta bugawa,da zaran ta shigo shi kuma yana d'aki,lokacin kuma da ta fita zai fito.... Yana kwance kamar wanda aka tsikara da allura ya mik'e parlor ya fito ya kwanta babu kowa cikin parlorn... K'amshin da yake jiyowa daga kitchen shi ya sa ya mik'e fuskarsa ta dad'a kyau saboda yanda tayi fayau uwa wanda yayi jinya,a bakin k'ofan ya tsaya ya jima yana kallonta,sam bata san da mutum a bayanta ba,ya jima a haka hannayensa a hard'e kan k'irjinsa..... MAMA ce ta fito cikin shirin fita da yake gidan ba kowa duk suna skul,kallon hanyan kitchen en tayi saboda ta ga kamar da mutum a tsaye,mamaki fal zuciyarta yanda ta ganshi yayi a gurin.... ''SON zan fita'' Tayi maganar cike da k'ulewa,aiko ya juyo a d'an firgice yana kame² ya dawo cikin parlorn,sam ya rasa wace kalma zaiyi amfani da ita gurin kare kansa,kansa ya d'an kawar gefe ''Allah ya kiyaye hanya'' Ya furta a hankali,da harara ta rakashi ta fice,nan ya kwanta yana d'an murmushi,duk wani shige da ficenta akan idonsa take yinsa,zuciyansa fal far in ciki.... ********* ''Tabbbb tun kafin wannan al'amarin ya afku gara nayiwa tufkar hanci'' Fad'in HAJIYA MURJA kenan da suke tafiya cikin motor ''Taya ma za ayi da raina maza biyu su nuna suna son wannan kuchakar yarinyar,ni kuma nawa suna zaune,ai sam haka ba zai tab'a faruwa ba,duk cikin su babu rabonki yarinya'' Wata k'awarta ta tuno take ko ta hau binciken number enta a wayanta............... *_~TEAM KHUBRA~_* *_REAL SMASHER._*🤞🏻😘 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *8/ʍɑվ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *2⃣4⃣* *D*a k'yar ta iya lalubo number matar,wata dariya tayi ita kad'ai tana sak'a abubuwa da dama cikin ranta,bata jira ta b'ata lokaci ba ta danna mata kira.... Ta jima tana ring ba a d'aukaba,haka ta ci gaba da mai²ta kiran kusan sau uku tana kira wayan na katsewa,har wata zuciyar ta bata shawaran kar ta sake kiran ta ji ba zata iya hak'uri ba,kiran ta sake yi,cikin sa'a wannan karon aka d'auka,zuciyarta tayi kar saboda murna,sai dai me tana d'auka taji an ce ''Hello! wa ke magana,naga an dameni da kira tun d'azun'' Baki ta sake tana mamakin lamarin dama akwai ranar da HAJIYA LAURA zata manta da ita haka,matar da tun k'uruciya suke tare... Zuciyarta ta danne tana fad'in ''HAJIYA LAURA amma alk'awari baice haka ba,yanzu a kwai ranar da zaki manta da ni k'awarki da muka tashi tun yarinta?'' ''Laaaa!HAJIYA MURJA kin san Allah wannan kalaman naki su suka sa nayi saurin ganewa,da yake sim card en nawa ya sha welcome back ne,saboda ana yawan sacemin waya ko na yar,to ke kuma ba gwanar kiran mutum ba bare na samu numbrki'' ''Eyyahh!Allah ya maida alkhairi'' ''Ameen''........... Nan suka gaisa,kafin HAJIYA MURJA ta soko mak'asudin kiran da tayiwa ita HAJIYA LAURAN,bata b'oye mata ko da wasali ba kan abunda ke shirin faruwa..... Dogon numfashi ta sauke,kafin ta cema da HAJIYAN ''Gaskiya HAJIYA yanzun bana so muyi saurin yanke hukunci,amma abunda ya kamata muyi shi KHALEED tunda gida d'aya kuke da shi da kanki zaki sa masa ido kan al'amuransa,tunda kinga har yanzun bamu gane sonta yake ko kuwa,shi kuma wancan KHALEEL kika ce sunan sa ko?'' ''Ehh!haka ne'' ''Yawwa to abunda za kiyi shi ne duk hanyar da zai ganta idan ya zo gidanki ki tosheta,sam kada ki ba shi wannan damar,idan yaso sai ki dinga tura su ASHNAR ko ita ZUHRA,idan kuma ya tambayi yarinyar kawai kice ai ta koma gidansu aure za su mata,fak'attt magana ta k'are kinga an yiwa tufkar hanci'' Shiru tayi tana sauraren k'awar tata,take ko tayi na'am da shawarar tata,sun jima suna magana kafin suka yi sallama kan sai kuma sun had'u ko ta sake kiranta..... 《《》》 Da ihuu su HANEEF suka shigo kamar kullum,sai dai suna shigowa parlor suka yi d'iff saboda ganin OGA a kwance,babu wanda yayiwa magana suka b'ace kowa yayi hanyan d'akinsa.... Allah sarki ZUHRA ko da ta shigo cikin parlorn waige² tai tayi coz sai da ta biya d'akin KHUBRAN bata ganta ba,hanyan kitchen tayi nan ta hangota ta juya baya,hakan yasa ta lallab'a bata sani ba sai ji tayi an rufe mata ido,y'ar dariya tayi mai sauti,itama ZUHRAN dariyan tayi kafin kuma ta zare hannunta daga fuskan KHUBRA,juyowa tayi ta kalleta ''Har kun dawo?'' ''Lallaima wai har,ina fa har,kina gani tun safe fa muka futa bamu dawo ba sai yanzun'' ''Ai kuwa dai kam,Allah ya bada sa'a'' ''Ameen kam,barin shiga na fito'' ''Toh!a fito lafiya'' Ta juya tana tafiya had'e da murmushi,har ta fice ita kuma ta ci gaba da aikinta..... Dai² ta zo giftawa ta parlor BB dake kwance ya d'an bud'e ido saboda yaji maganarta a kitchen ''My SIS idan kin fito ki zo ina nemanki'' ''To BBNAH'' Da sauri tayi ciki,cikin sauri² tayi wanka ta shirya,a parlorn ta tarar da shi,kusa da shi ta nemi guri ta zauna,parlorn daga ita sai shi ''Aaamm!MY SIS kin san me zan tambayeki?'' ''A'a YAYANAH'' ''Yawwa dama kan wannan k'awar taki ce,me kika sani dangane da ita?'' Yanayin tambayar ya d'an d'aure mata kai,ganin bata gane ba yasa ya mata bayani,y'ar dariya tayi kafin ta sake maimaita masa abunda ta sani game da KHUBRAN kamar lokacin farko da ta tab'a bashi labarinta...... ''Ok ba komai jeki na gode'' Yana gama fad'in hakan ta mik'e ta nufi kitchen,kasancewar ZUHRA yarinyace amma akwai basira ta harbo inda maganar BB ta dosa,dan tafi kowa sanin halayyarsa ta rashin shiga abunda babu ruwansa,idan ko har kaga yayi magana kan abu to da walakin (Goro a cikin miya)....... Kitchen en ta koma ta tarar har ta gama abunda take,da murnanta ko ta hau tsokanarta ''Matar YAYA har kin kammala ne,dan nifa da yunwa na dawo'' Da sauri KHUBRA ta kalleta tana mata alamar neman k'arin bayani ''Wane YAYA kuma?'' ''Nawa mana ko zan fad'i wani ne ba shiba?'' ''Uhmmm!rufamin asiri matsayina bai je nanba''..... ''Tabbb ai wollah har kin wuce nanma,ke wollah da izinin Allah ke rabon YAYANA ce dan ko naga alama''....... Maganar ce ta mak'ale saboda shigowar ASHNA cikin kitchen,kallon da ta yiwa ZUHRAN da ita kanta KHUBRAN shi ya tabbatar musu ta ji abunda suke magana akai.... Sai da ta gama d'aukan abunda ta zo nema sannan ta kalli ZUHRA ''Ke kam koi banza,ta ina ma zaki had'a YAYA da wannan matsiyaciyar,wacce iyayenta basu damu da sanin inda take ba,sun turota aikatau saboda neman abun duniya,ki rasa da wacce zaki had'a shi sai wannan,to wallahi yafi k'arfinta,banza sha³ kawai'' ''Eeehh!an fad'a en naga itama ai mutum ce,ke har kina da bakin magana,wannan en da kike gani kina rainawa naga dai ta fiki duk wani abu da kike tak'ama da shi,k'ark'ari ki nuna mata gidanku suna da wadata, bayan wannan babu abunda zaki gwada mata''...... Bata k'arasa ba ASHNA ta kwasheta da mari da yasa tayi shiru tana binta da kallon mamaki ''Ni kika mara kan na baki amsa?'' ''Duk ranar da kika sake min irin wannan maganar wallahi sai nayi miki wanda yafi wannan'' ''Tabbbb to wallahi baki isa ba,Allah yau babu abunda zai hanani ramawa'' Nan tayi kan ASHNA suka hau kokawa,ita kam KHUBRA sai hak'uri take basu,duk da maganar da ASHNA tayi kanta ranta ya sosu ganin suna fad'an kuma ta shiga k'ok'arin rabasu amma ina sunk'i rabuwa.... Hayaniyar da ya jiyo daga kitchen en shi yasa ya taso yana zuwa ya tarar dasu suna kokawa,tsawa ya kwad'a musu duka ''Uban me ya had'aku da zaku sa mutane a gaba kuna rigima?'' ''YAYA wai fa kan muna maganarmu shi ne daga zuwanta ta sa mana baki,dan nayi mata magana shi ne ta mareni'' ''Ai ke dama baki da hankali kullum girma kike kina dad'a cin k'asa,wawiya kawai zo ki b'acemin a nan ko na b'alaki'' Fitowa tayi tana turo baki k'asa² ta hau k'unk'uni,duk abunda take idanunsa na kanta,sai da ya bari ta zo zata gifta ta kusa da shi ya fizgota aiko nan ya shiga knocking kanta ''Ni nake miki magana kikema k'unk'uni ko?'' Ta kasa magana saboda azaba,ta sa hannayenta tana son k'are kanta ganin yak'i barinta ta hau masa ihuuu,k'afa yasa ya ture ta gefe ''Gobe ma idan na miki magana ki sake min irin wannan kiga yadda zanyi da ke sha³'' Da gudu ta bar gurin tayi d'aki sai kwala ihu take uwa wacce akace uwarta ta mutu..... Kallon ZUHRA yayi ''Ke kuma ki ci gaba da fitsara kinji,da dai ban sanki da wannan halinba,amma yanzun kin sauya hali'' Kanta a k'asa har ya gama abunda zaiyi ya bar gurin,kuka ZUHRA ta sa,matsowa tayi ta kamata ta zaunar da ita tana bata hak'uri itama kamar za tayi kukan ''Kinga kiyi shiru kije ki bashi hak'uri kar yayi fushi da ke,kina ganin dai yanda ya bar nan'' Shiru tayi ta hau goge fuskanta,bin bayansa tayi a parlor ta tarar da shi ya dafe kansa da hannu,a k'asa ta zauna dai² kusa da k'afafunsa ''Pardon please BB'' Shiru tayi tana neman kalmomin da za tayi amfani da su ''Allah YAYA ka yadda ni ba rashin kunya nayi mata ba'' Shiru yayi mata baice komai ba,ita kuma hakan da yayi yak'i mata magana tasa masa kuka.... A hankali ya bud'e fuskansa,tashi yayi ya zauna ''Ya isa haka,amma abunda bana so ki dena biye mata kuna wannan shirmen kinji ko?'' ''In Allah ya yarda bazan sake ba'' ''Yawwa to goge fuskanki'' Goge fuskanta tayi,kafin ta mik'e ''Na gode YAYANA'' Murmushi ya mata,ita kuma ta juya ta bar gurin........ 《《》》 Tun da ya fice bai koma gidan ba sai dare sannan ya shigo gidan,babu kowa a parlor haka ya lallab'a ya shige bed room ensa,yana shiga ya rufe door en ko light en d'akin bai kunna ba haka ya gama abunda zaiyi ya kwanta.... Da safe ko bai bari sun had'u da UMMI ba yayi saurin ficewa.... Yau kwana uku kenan UMMI bata sa KHALEEL a idonta ba,abun duniya duk ya dameta,tun safe ta fito amma tana duba d'akinsan ta tarar har ya fice,kuma ta tabbatar a gidan yake kwana,yau kam ta k'udurce duk tsayin lokacin da zai shafe zata jira don magance matsala.... Tun da ta nemi guri ta zauna bata ko tashiba,duk abun da yayi ya dameta,ko sallah za tayi a nan cikin parlor take yi duk dan kada ya shigo ba ta saniba..... 《《》》 Shigowarta kenan cikin gidan,aiko muryanta kad'ai ASHNA ta jiyo tayo waje tana kuka uwa yanzun ne abun ya faru.... Tana zuwa ta fad'a jikin MAMA tana gunjin kuka,kallonta MAMAN tayi tana fad'in ''Me aka miki?me ya faru?maza sanar da ni'' Kasa yin magana tayi sai kuka take kamar ana zarar ranta,rarrashinta MAMAN tayi har sai da tayi shiru sannan ta hau fad'in k'arya da gaskiya duk ta sanar mata,aiko ranta iyayi million ya b'aci ''Yi shirunki dama abunda nake hasashe kenan amma ba komai yi shiru karki damu kinji y'ar lele'' Dariyar kissa tayi tana fad'in ''MAMA dan Allah ina YAH KHALEEL,yaushe zaki je gidan su?'' ''Uhmmm!ASHNATA kenan mene kike tambayarsa?'' ''Babu komai MAMA kawai tambaya nayi'' ''Fad'amin dai in da wani abu'' Da gudu ta bar gurin tana dariya,ita ko MAMA dariya kawai tayi tana kallonta....... 《《》》 K'arfe 1:00am ya shigo gidan,tafiya ya ci gaba da yi a cikin parlorn,sai da yazo tsakiya yaga haske ya gauraye cikin parlorn,juyowa yayi yana kallon cikin parlorn.Tsaye yaga UMMIN nasa wani kallo da ta yi masa shi yasa shi sunkuyar da kai k'asa ''Yanzu SON abunda kayi ka kyauta kenan?akan wannan maganar za kayi fushi da ni?shi kenan duk abunda kaga ya dace da kai kayi kaji?'' Ji yayi gaba d'aya jikinsa yayi sanyi,sam ya kasa motsawa daga gurin,har tayi ta gama fad'an da zatayi masa,kansa a k'asa ya fara tafiya da k'yar har ya zo gabanta,durk'usawa yayi har k'asa ya rik'e k'afafunta.Gafaranta ya shiga nema da yake ba ta da rik'o ta yafe masa... ''SON maza je ka kwanta gobe in sha Allah zamu je gidan HAJIYA MURJA duk abunda kake so nima ina sonsa matukar bai kaucewa hanya ba,kuma bai sab'awa addini ba''.... ''Yawwa UMMINA na gode sosai,shi yasa nake sonki'' Ya bata peck a kumatu ya fice yana mata sai da safe,farin cikin dake kwance kan fuskarsa shi ya bata nutsuwa tayi murmushi,kafin ta bar parlorn ta nufi bed room enta..... 11:45am ya fito cikin shirinsa,k'ananan kaya ne a jikinsa tun daga parlor yake kiran UMMI dai² ta fito daga d'akin take fad'in ''Kai SON ban sankafa da fitsara ba,irin wannan kira haka kamar wanda zai bar garin,saurin me kake yine?'' ''Uhmmm!Allah UMMI bana son rana tayi mana ne'' ''Za dai ka fad'i gaskiyama'' Dariya yayi yana yin gaba,ba tare da ya furta komaiba,cikin minti goma sha biyar suka iso gidan... A parlor suka tarar da yaran,nan ko suka shiga gaida su,ASHNA sai kallon KHALEEL take wanda baima san me take yi ba,da sauri HAJIYA MURJA ta fito tana fad'in ''Maraba da zuwa,ina fad'in zanzo ashema zaki rigani zuwa'' ''Uhmm!ai kuwa dan ko d'anki ne ya tasoni ba zuwana bane wannan zuwansa ne'' Y'ar dariya ta yi suka shiga d'akinta,sun gaisa a mutunce,kafin HAJIYA FATEE ta sanar mata da dalilin zuwan nasu.A ranta kam sam bata ji dad'in maganar ba,amma a fili sai ta nuna mata babu komai,nan suka ci gaba da fira kamar babu komai a ranta.... 'Ban garen KHALEEL da BB kuwa,a bed room ya tarar da shi yana kwance,shigowansa yasa ya tashi ya nufi hanyan toilet yana shirin shiga wanka,sun gaisa ya juya zai shige KHALEEL ya dakatar da shi ta hanyar fad'in ''Yeahhh!ka fara tayani murna kafin ka wuce mana ko so kake ka barni nan da kad'aici?'' 'Dan juyowa yayi ya kalleshi,wucewa yayi zai shige kalaman KHALEEL suka dakatar da shi ''Haba mana YAYANMU ai sai ka''....... Bai k'arasa ba ya juyo ya kalleshi ''Ai kai kam baka da girma,mene kuma na wani cemin YAYANKU banda iskanci irin naka YAYANKU kai da wa?'' ''Ni da abar k'aunata mana'' 'Dan dawowa yayi ya zauna kusa da shi ''Ka ce mene,wa ce kuma haka?'' ''Wannan k'anwar taka fa nake nufi'' Yayi maganar yana kwanciya da baya saman bed en,yana rufe ido ''Ai kam ban san me kake fad'a ba'' ''Da Allah wannan balabiyar nake nufi'' Ido ya fito waje coz ya gane inda maganar tasa ta dosa,mik'ewa yayi baiyi maganaba,ya sake tafiya zai shiga toilet en coz ya d'an fara jin haushin maganar ''Banza ne kai ai idanma baka so to barin sanar da kai tunda ba kai zaka bani ba.....Yauma dalilin da yasa kaga UMMI kan maganar ne''........ Cikin tsawa ya juyo yana fad'in ''What?'' Tambayar ce ta sa KHALEEL d'agowa ya kalleshi yanayin da yagan shi ciki shi ya bashi tsoro,kasa magana yayi kawai ya juya a fusace ya shige toilet en had'e da turo k'ofan da k'arfi,abunda yayi ne ya bawa KHALEEL mamaki ya bi k'ofan da kallo zuciyansa fal tunani........... *#Huh! Don't imaging coz yanzun aka soma,chakwakiya na gaba....* *_~TEAM KHUBRA~_* *_REAL SMASHER._*🤞🏻😘 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *10/ʍɑվ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *2⃣5⃣* *K'*asan shower yayi still ruwa sai sauka yake a jikinsa yana zubewa,sam ya kasa samun nutsuwa,gaba d'aya haushin KHALEEL en yake kan wannan maganar da ya zo masa da ita,shi kam duk da yasan abunda zai faru kenan a zuwansu gidan da yayi fatanma bai ga wannan ranar ba,tunani duk ya dame shi,kusan mintuna ashirin ya d'auka a haka hannayensa dafe jikin wall en toilet en.... Da k'yar yayi wankan,bakinsa yaji kamar yana masa d'aci saboda b'acin rai,zuciyarsa ko uwa za ta fito,haka ya b'ata lokaci cikin toilet en kafin ya fito d'aure da towel,jikinsa kad'ai ya goge ya saka kayansa,car key ensa ya zara kan mirror face ensa a murtuk'e yayi hanyan ficewa daga bed room en ba tare da ya san inda zai nufaba...... Duk abunda yake yi idanun KHALEEL na kansa,sam ya kasa ganema kansa dalilin da yasa ya zuba masa na mujiya kenan,sai da yaga yana shirin fita tukun ya furta ''Ina kuma zaka je kabarni nan?'' A d'an fusace ya juyo ya kalleshi ''Ka aikeni ne da zaka tambayeni?'' ''No!Allah ya baka hak'uri,amma banyi da niyyan b'ata maka rai ba'' Juyawa yayi zai fice har ya murd'a handled na door en KHALEEL ya taso ya biyo bayansa ''Man wai me yake faruwa,na ganka ba kamar yadda na sameka ba'' Yana tafiya yake fad'in ''Mene ka gani?'' ''Please tsaya muyi magana kafin ka wuce'' ''Bani da time yanzun letter ma had'u'' Yana gama maganar ya sa kai ya fice,da mamaki a fuskan KHALEEL ya raka shi da ido,shi dai yasan lafiya k'alau ya tarar da shi amma bai san me ya jawo chanjin da aka samu ba.. Phone ensa ya duba sai dai ya tuna ya barota cikin mota,haka ya zauna cikin parlor yana hasashen laifin da yayiwa KHALEED en da yasa ya canza masa lokaci guda... Yana zaune ZUHRA suka shigo sai dariya suke da yake basu san ya zoba sai yanzun da suka shigo,a ladabce suka gaisheshi kafin sukayi kitchen.. Kallonsu yayi lokacin suna wucewa,a zuciyarsa ko yana sak'a abubuwa da dama game da KHUBRAN,sai yanzun zuciyarsa tayi sanyi ko dan arba da yayi da ita,duk da bata bari ya k'are mata kallo ba,har suka b'acewa ganinsa,sannan ya juyo.... ASHNA dake zaune duk abunda yake hankalinta na kansa,duk ji tai tana jin haushin ZUHRA da KHUBRAN ko dan kallon da taga KHALEEL en nayi musu,musamman ma KHUBRA da taga yafi tsananta kallonta.... Duk ta gama kumbura uwa zata fashe kan haushin da take ji,kawai dai dan bata da yadda za tayi ne,shi yasa take zaune har yanzun cikin parlorn..... Zaman gurin duk ya isheshi bama kamar zamansu da wad'annan halittun,da ko kad'an bai son ganinsu kusa da shi,fuskarsa ya dad'a tamkewa yana ta spinning car keys.... Fitowar UMMI ne yasa ya d'anji sauk'i dan kam dama zaman ya isheshi haka,mik'ewa yayi yana jiran k'arasowarta,da zuwanta gurin ko suka yiwa MAMA sallama suka fice.... Wani banzan kallo MAMA ta rakasu da shi,tana fad'in da ni kuke zancen,wallahi bazan tab'a barin wannan al'amarin ya faruba.... 《《》》 Suna tafe a motan duk sunyi shiru,shi da abunda yake tunani,ita kuma UMMI shirun da tayi nemo hanyan da zata sanar da SON en nata matsalar da ake ciki take sonyi... ''Ammm!SON kasan me nake so da kai?'' Nodding kansa yayi ''Yawwa abunda nake so da kai,duk abunda za kaji yanzun,ka d'aukeshi a matsayin k'addara kaji ko?nasan ka da hak'uri amma ina so ka k'ara'' Gaba d'aya hankalinsa yana kanta ya rasa dalilin da yasa take masa wannan maganar ''Ka nutsu tukun muje gida zan maka bayanin komai kaji koh'' Kai ya sake kad'awa,yana driving amma hankalinsa sam baya tare da shi,driving en kawai yake haka har suka k'arasa gida.... 《《》》 Fitowarsa daga cikin gidan ransa duk a jagule,hakan yasa ya rasa ina zai nufa,rashin sanin madafa shi ya haddasa masa fasa fitan,direct ya nufi guarding duk ji yake garin ya d'aure masa wani zafi yake ji a jikinsa wanda bai san dalilinsa ba,sam ya kasa tunanin komai baya ga tuk'uk'i da yake jin zuciyarsa ke masa babu abunda yake ji,haushin kowa yake ji a yanzun...... Kasa zama yayi take ko ya kwanta saman grasses en da ke wajen,duk da rana da ta bud'e sosai a garin sai dai kuma guarding en bishiyu sun masa rumfa ta hakane kad'ai yasa babu rana cikin gurin.... Addu'ah yake kada Allah ya nuna masa irin wannan ranar mai cike da tarin k'unci,tsawon lokaci yana kwance a gurin bai sanma lokacin da su KHALEEL suka bar gidan ba,idanunsa ya kulle da suka sauya launi zuwa jaa saboda jin kansa da yayi tamkar zai tsage...... 《《》》 A parlor suka yada zango,kansa a k'asa duk damuwarsa bai wuce sanin abunda UMMI ke shirin fad'a masa ba,maganarta ce ta dawo da shi cikin duniyarsa... ''SON abunda yasa nace maka ka nutsu maganace da ta fito daga bakin HAJIYA MURJA wanda bana tsammanin akwai k'arya cikinta,kuma ban son b'oye maka,nafi son kasan gaskiyar zancen'' 'Dan kallonta yayi jin ta ambaci sunan HANIYAN KHALEED ''A halin da ake ciki kuma a yadda ita HAJIYAN ta sanarmin shi ne,yarinyar da kamin magana akanta ta riga ta koma garinsu,dan ta cemin iyayenta suka nemi ta koma za suyi mata aure cikin wannan satin''........ A tsorace ya kalli UMMIN nasa yana fad'in ''Wallahi UMMI k'arya ne'' Tsawa ta buga masa wadda tasa ya shiga hankalinsa ba shiri yayi shiru ''A gaban idona kake k'aryata ta,ko babu aminci tsakaninmu ya kamata ka fad'i wannan mummunar kalmar a kanta,idan na sake jin ka furta irin wannan maganar sai ranka yayi mummunan b'aci'' Cikin fusata take maganar wanda yasa shi sunkuyar da kai yana fad'in ''Ki gafarce ni UMMINA amma wallahi sam wannan maganar ba haka take ba,dan kuwa da idona na ganta yanzun,kawai dai a kwai wata manufa tata da yasa ta fad'a miki haka''.... Zuciyarsa fal b'acin rai dan shi kam wallahi shi kad'ai yasan me yake ji,taya ma za ace wani za ayi mata aure kuma cikin wannan satin amma kuma tana zaune cikin gidan bata koma nasu ba,tabbas shi kam ya san shiri ne da wata a k'asa... Kalamai masu taushi UMMI ta shiga fad'a masa tana masa nasiha,har ya samu yaji zuciyarsa tayi masa sauk'i,kafin ya mata sallama ya fice daga gidan...... 《《》》 Guri ta samu ta zauna bayan sun b'acewa ganinta,lokacin ne kuma muryan ASHNA ta dawo da ita daga kogin tunanin da ta tsunduma duk kan neman mafita ta wannan al'amarin dake shirin jagule mata..... Tana shirin magana BB ya shigo da ganin yanayinsa ba sai ka tambaya ba za kasan yana tattare da matsananciyar damuwa.... Kallonsa MAMA tayi a tsorace take binsa da kallo danko ba k'aramin firgita tayiba da ganin yanayin nasa,kiransa tayi babu musu ya nemi guri ya zauna yana dafe kansa dake barazanar fashewa.... ''SON me yake damunka,kaga kuwa yanda halittarka ta sauya lokaci k'ank'ani,maza sanarmin me yake faruwa'' ''Babu komai'' Ya fata cikin cool voice nasa ''A kwai abunda kake b'oyewa SON'' ''Babu fa,kawai ina jin headache ne'' ''Eyyahh!Allah ya sawak'a maza ASHNA duba kawo masa magani idan ya sha sai ya kwanta ciwon zai sauka'' A zuciyarsa yake fad'in ''Tabbb!ai duk duniya yanzu kam ciwona baida maganin da ya wuce jin gaskiyar maganar da KHALEEL ya fad'amin'' ''Wace magana kenan SON?'' MAMA ta tambaye shi,sai lokacin ya d'ago baki ya sake, kenan a fili yayi maganar ko me? ''Babu komaifa MAMA'' ''Toh shi kenan ai kai kam dama haka kake da masifar zurfin ciki ba a tab'a gane kanku kai da ZUHRA sai kuyi tayi wata rana sai ciwo ya hallakaku'' Shi kam kallonta kawai yake ya kasa magana,harara ta cilla masa shi abun na MAMA wani lokacin har dariya yake bashi,sai dai wannan lokacin babu halin yi saboda baya cikin mood en da zai yin...... ''Ko ka fad'a ko kada ka fad'a magana KHALEEL ya fad'a maka kan waccan yarinyar nasan dai bazai wuce haka ba,to wannan maganarma ba mai yiwuwa bace,dan ko na fad'a musuma aurenta za ayi a garinsu cikin satin nan'' Maganarta ta k'arshe ce ta dakatar da shi daga nutsuwar da ya fara samu,da sauri ya kalleta da jajayen idanunsa ''Dagaske MAMA?'' Yanayin da ya mata tambayar yasa ta tsaya tana wani nazari a kan fuskarsa,shi kuma ganin ta k'ureshi da ido yasa ya tashi ya bar wajen ba tare da ya sake kallon kowa cikin parlorn ba.... ASHNA ce ta kalli MAMA ''Kin gani ko MAMA dama wallahi na fad'a miki akwai abunda yake nufi da yarinyar can,tun ranar da ya dakeni akan maganar da naji ZUHRA sunayi da ita,Allah MAMA kada ki barima wannan abun kunyar ya faru..... Numfasawa tayi tana kallon ASHNAR tana kad'a mata kai ba tare da ta furta komaiba ta bar parlorn..... 《《》》 Tun da ya fita ya barta take tunanin maganganunsa.... Wane dalili ne zai sa HAJIYA MURJA tayi mata k'arya kan wannan maganar,tunani iri daban-daban sai bijiro mata suke wanda ta rasa amsar su.... Idan ko abunda KHALEEL ya fad'a mata haka yake tabbas akwai manufar da yasa HAJIYA MURJAN tayi mata haka,sai dai koma mene ne ita ta sani,babu damuwar komai a ranta ta kauda tunanin wannan lamarin tana barin parlorn..... 《《》》 Shigowansa bed room en ya kwanta yana pacing ceiling... Ta wani b'arin na zuciyarsa yana jin nutsuwa na saukar masa,sai dai kuma ta wani gefen yana jin tsoro wanda ya rasa dalilinsa,yana wannan tunanin bacci ya d'aukesa..... 《《》》 Can ta k'ule a bed room enta,number HAJIYA LAURA ta shiga kira,bugu biyu aka d'auka,a daddafe ta tsaya suka gaisa,aiko nan ta shiga koro mata jawabai na abunda ke shirin faruwa,yanayin da ta ga KHALEED a yanzun,da maganar da UMMIN KHALEEL ta zo mata da shi,bata rage mata komaiba ta sanar da ita...... Dogon ajiyar zuciya ta sauke,tana fad'in ''Ni kam na rasa me yaran nan suka gani jikin k'aramar yarinya da suka rud'e haka,kome take da shi ai muma y'ay'anmu nada'' ''Uhmmm!HAJIYA LAURA kenan kawai dai ayi sha'ani(wai akace na birni ya zagi na k'auye),wallahi dan baki ga yarinyar bane,ni kaina yarinyar na bani tsoro duk lokacin dana kalleta,bama kamar yanzun a hakama wollahi bata fita ko ina nasan da na wajenma haka za suyita biyota mukuma namu suna jibge a gida (uwa ragunan layya)'' ''Bari ke dai maganinsu za muyi cikin lokaci kad'anma kuwa,amma ki bar komai a hannuna,duk abunda ake ciki zan sanar miki zuwa dare''.... Da haka sukayi sallama,wani murmushin mugunta tayi tana bin wayan da kallo..... Suna gama wayan ta shiga contact enta wani number tayi dialing,tana yin ring aka d'auka ''Allah ya taimaki HAJJAJU'' ''Ammmm!BIGGY ba lokacin wannan wasan yanzun so nake kayi maza ka zo ina son ganinka'' ''An gama ranki shi dad'e...... K'it ta datse kiran....... In less-than fifteen minute's ya k'araso gidan cikin wani k'aton jeep black colour,baka iya hango komai na cikinta,motan na gama tsayuwa aka bud'e back seat na motan,wani zabgegen mutum ne ya fito kakkaura,da ganinshi kaga manyan basawa.... Cikin gidan ya nufa fuskarsa babu annuri a samanta,yana shiga y'ar aikinta dake parlor ya kalla yana fad'in ''HAJIYA fa'' ''Tana ciki barin kirata'' Ta mik'e da sauri ta nufi hanyan d'akinta ''HAJIYA kinyi bak'o'' ''Ina zuwa'' Ta fad'a ita kuma yarinyar tayi waje,bayan yarinyar ta biyo tana tafiya irinta hamshak'an mata,a tsaye ta tarar da shi ya juya baya ''Yawwa BIGGY aiki ne zan sa ka,amma nasan ba mai wahala bane a irin aikinku,a kwai yarinyar da nake son ku d'auke nisanta nake so kuyi da ita daga garin nan,koma inane ku kaita ba ruwana,wannan shi ne aikin'' Wata mahaukaciyar dariya yayi saboda raina aikin da yayi ''Yo HAJIYA wannan aiko yarana za suyi ba sai niba'' ''Nasan da haka BIGGY ai shi yasa bana wasa da lamarinka,zan turo maka address na inda gidan yake'' ''An gama,sai na jiki'' Da haka ya sa kai ya fice.... Yana tafiya ko ta tura masa komai,take kuma ta kira HAJIYA MURJA ''Toh na gama nawa sauran aiki yana hannunki,duk yanda za ayi anjima bayan Maghreb ki aiketa,zan miki bayani bayan kinyi hakan'' Tana gama fad'in haka ta kashe wayan,tana wani makirin murmushi........ *7:30pm* KHUBRA ta shigo parlorn HAJIYA MURJA ita kad'ai ta tarar a parlorn,wani leder bak'i ta mik'o mata k'unshe da wani abu da ni kaina ban san mene a ciki ba,amsa tayi kafin HAJIYA ta soma magana ''Maza karb'i wannan kije waje zaki ga wani a bak'in mota ki kai masa injini'' Cike da ladabi ta amsa,har ta mik'e ZUHRA ta fito daga corridor en bed room nasu,kallon KHUBRAN tayi itama tana kallonta tana d'an murmushi kamar wanda basu saba ganin junaba suka k'urawa juna ido,fitowan BB ta waiga ta kalle shi,rana ta farko kenan da ta k'ure shi da kallo a iya zamanta a gidan,tsananin fad'uwa taji gabanta yanayi,a hankali ta waiwaya za ta fita,haka kawai taji idanunta sun kawo ruwa,da sauri ta sa hannu ta goge... ''SIS tsaya na rakaki'' Bata jira amsanta ba ta biyo bayanta,da sauri ta rik'e hannunta har suka fita daga gidan,KHUBRAN ce ta k'arasa kusa da window en motern tayi knocking,ZUHRA kuma tana jikin get,k'ofan aka zuge.... Gaisheshi tayi duk bashi da kad'ai ne a motanba,amma ita kam shi ta gani ta mik'o masa abunda ke hannunta aiko take ya mik'a hannu kamar zai amsa kawai ya fizgota cikin motan take ya datse k'ofan suka figi motan a 360............................... *_~TEAM KHUBRA~_* *_REAL SMASHER._*🤞🏻😘 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *11/ʍɑվ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~________________________~* _Ga masu buk'atar son kasancewa da group na *Y'AR GARUWA* za ku iya yin joining ta hanyar amfani da wannan link en,saboda gujewa had'uwa da maza,mata zallah dan Allah👏..._ 👇 Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/EvdAvnFbBaX2BBMAwCCH4E *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *2⃣6⃣* *B*akinta da hancinta ya danne da wani handkeey take ko ta sulale uwa matacciya.... Ganin abunda ya faru yasa ZUHRA dake tsaye matsowa da gudu kuma ta hau natsowa kusa da motan... Cikin wani razanannen murya ZUHRA ta shiga k'wala kiran sunan KHUBRA wadda tuni motarsu har ta b'ace daga line en..... Faruwar hakan ke da wuya ta dawo da gudu ta shiga gidan babu kowa cikin parlor sai BB dake shirin barin gurin shima,a rud'e ta k'arasa kusa da shi fuskanta duk ya gama yin kacha² da hawaye,chakumoshi tayi tana kuka take fad'in ''Sun tafi da ita dan Allah YAYA karka bari su tafi da ita'' Gaba d'aya kalamanta sun gama rud'ashi,ya rasa ganema inda ta dosa,a hankali ya shiga girgizata dan kam ya gama fuskantar a kwai matsala ''Su waye ne kam,kuma waye suka tafi da ita?'' ''YAYA KHUBRA sun tafi da ita,YAYA za su cutar da ita,please karka bari su gudu da ita'' Sunan KHUBRA da ta ambata shi ya masifar d'aga masa hankali,take ko ya sake ta yayi hanyan fita daga gidan,da gudu ta biyo bayanshi,sai dai ko da ya fita babu ko da k'urar motan bare yasa ran ganin ita kanta motan,tsayawa yayi ya dafe kansa baya ga *''INNALILLAHI WA-INNA ILAIHI RAJI'UN,ALLAHUMMA AJIRNIY FIY MUSIBATIY WA-AKLIFNIY KHAIRAN MINHA''* babu abunda yake fitowa daga bakinsa sai wannan,wani sabon yanayi ya tsinci kansa a ciki,sam ya kasa magana fuskarsa lokaci guda har ta sauya kammani.... ZUHRA dake tsaye kusa da shi ko har yanzun banda gunjin kuka babu abunda take,kallonta kad'ai ya iya yi,kusa da ita ya matso yana son tambayanta sai dai kalmomin sun mak'ale a iya mak'oshinsa..... Matsawa yaga ZUHRA na yi har dai² gurin da motan su BIGGY ta bari,takalman KHUBRA ta d'ebo wanda garin kokawar sata a motan suka watse a kasa,rik'esu tayi k'am ta rungume tana ta faman kuka,gwanin tausayi haka take kukan babu mai rarrashi.... Kusa da ita ya dawo hannayensa yasa akan sholders enta ''Pleasee!ya isa haka sisnah waye ya sa ku fito a daren nan?'' ''MAMA ce ta aikomu'' Katseta yayi dan ko sunan kad'ai da ta ambata sai da gabansa yayi mugun fad'uwa,a zuciyarsa ya furta ''Ko me ya sameki tabbas da sa hannun MAMA a ciki,amma me yasa za ta aikata mata haka?",rashin amsa ya sashi dakatar sa tunanin,dan ko ba lokacin tunani bane,gefe suka sake komawa cikin low voice yake mata magana,ammafa hankalinsa baya tare da shi ''SIS abunda nake so dake ki dena kukan nan haka,kuma koda mun koma gida kada ki nuna damuwa kan abunda ya faru,har sai mun gano gaskiyar wanda ya aikata hakan'' ''YAYA ai babu wanda ya aikata komai face MAMA'' Duk da ya sani da sauri ya dakatar da ita ''A'a SIS ba a saurin yanke hukunci,mu jira mu gama bincike tukun kin ji ko?'' Kai ta kad'a masa,hannunta ya ja suka kama hanyar komawa cikin gidan suna tafe yana bata baki kan kada ta kuskura ta nuna damuwa ko da anzo ana maganar a ganta.... A hanyan suka rabu shi ya nufi corridor da zai sada shi da bedroom ensa,suna tafe kowa zuciya babu dad'i kamar majinyata haka kowa ya shiga bed room ensa..... Daren ranar kam a b'angaren ZUHRA da BB babu wanda ya iya cikakken bacci,gani suke kamar an had'e musu darare arba'in dan ko har fatan wayewar gari suke..... 《《》》 Tun bayan barinsu line en basu tsaya ko inaba sai k'auyen ZAKIRAI dake cikin garin kanon dabo,da yake dare ya soma yi sosai kuma suna son komawa dan ko hanya suke shirin d'auka zuwa garin kaduna,dai² kasuwarsu dake gefen hanya suka perker,sai da suka duba suka tabbatar babu kowa da yake ganinsu kafin suka kinkimota daga cikin motan,k'asan wata rumfa suka shimfid'eta tare da sanya mata ledan da ta fito da ita a tsakanin hannayenta,juyawa suka yi da mugun gudu suka bar gurin,yayinda KHUBRA ke baccinta peacefully,ko sanin inda kanta yake bata yi ba..... Sai da gari ya gama haske mutane nata hada-hadar kasuwanci sannan ta farka,nan ta shiga k'arewa ko ina kallo,can ta kalli kanta sai a lokacin ta iya tuna abunda ya faru da ita a jiya da dare,take ko wasu zafafan hawaye masu k'una suka shiga sakko mata,ta jima tana kuka uwa baza ta dena ba,da k'yar ta mik'e ta nausa cikin kasuwar k'afarta ko takalmi babu,ita dai har yanzun tana rungume da wannan ledar..... Yunwa ce ta fara damunta take ko ta sake sakin wani sabon kukan,tuna yadda rayuwarta ke garawa bisa doron K'ADDARA,zuciyarta fal addu'ah ta neman agaji daga mahaliccin sammai da k'assai,a hankali ta ware ledan dan duba abunda ke ciki dan kam ita tunanin yasarwa take,kud'i tayi arba da shi y'an one thousand sababbi,take ko tayiwa Allah godiya.... Guda ta zaro ta shiga bulayin neman abunda za ta karya,mai k'osai kad'ai ta samu aiko take ta tsaya sai dai gurin akwai yalwar mutane dake faman bin layi.... Kallo ne ya koma sama (wai akace shaho ya d'auko giwa) duk inda ta gifta sai dai kaga idanun mutane a kanta,bama kamar gurin mai k'osan da take tsaye uwa wacce aka dasa,har lokacin k'afafunta babu takalmi,tana nan tsaye har layi ya zo kanta mik'a kud'in tayi tana jiran a bata ba tare da ta fad'i adadin na yanda za a bata ba,kanta a k'asa ta kasa kallon kowa zuciyarta ko tarin k'unci ne a cikinta bama kamar yadda take fama da tunanin ZUHRA sahibarta,k'awarta,take ko wasu sabbin hawayen suka sake sakko mata.... Mai k'osai tana tambayarta amma sam bata sanma me take yiba,ganin haka yasa kawai ta auna mata,kafin tasa aka tab'ata,a d'an tsorace ta d'ago hannu tasa ta amsa tare da juyawa za ta bar gurin,chanjin da ta juyo da niyyar bata taga har ta yi gaba da sauri tasa wani yaro ya bi bayanta,d'an murmushi ta masa duk da tarin k'uncin dake cunkushe a zuciyarta ta amsa wash hawayen na dad'a sakko mata taci gaba da tafiya.... K'asan wata bishiya ta zauna jama'a nata kallonta amma sam hakan bai wani d'aga mata hankali ba,sai da ta tabbatar ta k'oshi kafin tunanin neman mafita ya fad'o mata.... ''Ina ya kamata na dosa ni da ba ko ina na sani ba?'' Babu inda ta sani bare ta ce ga hanyar gidansu,ko da canma ba fita take ba bare daga baya da ta dawo wani gari na daban,tana zaune ta had'a kai da gwuiwa tana tunani,wani mai kuran ruwa ya d'an tsaya a kanta ''Yarinya sannu ko'' Kallonsa kad'ai ta iya ba tare da ta iya magana ba,kamar mai nazarin wani abu take kallon gurin da take zuwa wani lokaci kuma ta sake kallon mutumin ji tayi ta aminta da shi take kuwa ta bud'e baki da niyyar yin magana....... 《《》》 Haka gari ya waye musu babu wanda yayi isashshen bacci idanunsu a soye,kasa fitowa suka yi su duka biyu.... Lokacin break yayi y'ay'an HAJIYA suka fito da niyyan break,sai dai suna zuwa suka tarar da gurin wayam babu komai,kowa sai tura baki yake gaba uwa shantu,suka nufi d'akin MAMA da niyyar yi mata k'orafi.... ''MAMA kinga fa ba a had'a break ba har yanzun'' Abunda ya fito daga bakin FATAHIYYA kenan da take kan gaba gurin shiga d'akin K'wak'walwar MAMA ta tafi yajin aikin ina kuma KHUBRAN ta shiga (ni da nake gefe nace kajimin y'ar cin)......... Ta jima d'age da kai tana tunani,kafin ta soma tunanin me ya faru da ta aiketa jiya? ''Kuyi hak'uri kunji,maza kuje ku sha ko tea ne kafin na fito'' Fita suka yi suna tura mata baki,sai k'unk'uni suke,suka nufi dinning area,flask en suka kinkimo a tunaninsu a kwai wani abu cikinsa nan ko suka tarar da shi wayam shima,kuka kad'ai su HANEEF suka sa,wanda sanadin haka yasa BB fitowa fuskarsa uwa wanda bai tab'a dariya ba,wani kallo ya watso musu wanda yasa suka shiga hankalinsu ba tare da ya furta komai ba... Cikin parlor ya kwanta idanunsa a rufe jijiyoyin kansa sun gama bayyana a fili,shi kad'ai yasan abunda yake ji a zuciyarsa,yanzun kam ko magana baya jin zai iya yi ''To amma ai bai kamata na ci gaba da zama ba yanzun,,,,,,,,me ya kamata nayi?'' Yayiwa kansa tambayar,saurin mik'ewa yayi ya koma bed room ensa,cikin abunda bai fi mintuna biyar ba ya fice daga gidan gaba d'aya..... ZUHRA kam kasa fitowa ma tayi tana d'akinta,kuka take sosai tamkar wacce uwarta ta mutu,idanunta duk sun kumbure sun canja launi kan kukan da tayi,sai da ta ji cikinta tamkar babu komai ta fito da k'yar tana tafe tana bin bango har ta shiga kitchen... Kallonta suka yi ganin yadda take bin bango,da ka suka tambayi juna sai dai babu amsa... Kitchen ta shiga kallon gurin da KHUBRA ta saba tsaiwa tana aiki ta shiga yi,take wasu hawayen suka k'ara b'alle mata ganin babu KHUBRA cikin gurin da suka saba zama tare,sai da tayi kukan mai isarta da k'yar kuma ta iya dafa indomie a plate ta juye ta d'auka tayi bed room enta..... Kallonta suka sake yi,coz tun tana cikin kitchen en suke jiyo k'amshi na tashi,gaba d'aya sun rashe suna jiran ta gama ta basu,aiko tana barin gurin suka shiga da sauri suna dubawa... Wayam babu komai ciki haka suka janyo tsummokaran k'afafunsu suka fito,guiwoyinsu a sake.... 《《》》 Fitarsu daga d'akin ta sauke wani gwauron numfashi,wayarta ta janyo ta shiga kiran HAJIYA LAURA... Bata wani jima tana ringing ba ta d'auka cike da izza da k'asaita kamar d'iyar sarauta.... ''Aiki yayi kyau mutuniyata,yanzun kam yaranmu sai yanda mukayi da su''... ''Ban fuskanci me kike nufi ba'' HAJIYA MURJA ta tambaya cike da zak'uwa da son jin labarin... Take ko ta zayyane mata sawa tayi aka d'auke KHUBRAN daga garin,ta k'arashe zancen da fad'in ''Nasan yanzu kam tayi nisa da mu'' Wata dariya ta saki ta makiran mutane.... Sai lokacin hankalin HAJIYA MURJA ya kwanta tana fad'in ''Mun rabu da alak'ak'ai,jarababbiya aje can a k'arata''.... Tana sakin dariya itama,sun jima suna shirya makircinsu kafin suka yi sallama.... *_~TEAM KHUBRA~_* *_REAL SMASHER._*🤞🏻😘 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *14/ʍɑվ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~________________________~* _Ga masu buk'atar son kasancewa da group na *Y'AR GARUWA* za ku iya yin joining ta hanyar amfani da wannan link en,saboda gujewa had'uwa da maza,mata zallah dan Allah👏..._ 👇 Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/EvdAvnFbBaX2BBMAwCCH4E *~________________________~* 🍟🍟🍟🍟🍟 🎂 *HAPPY BORN DAY*🎂 _OUR SURIKI *HASSAN ATK*_ 🎊 🎉🎉🎉 _A birthday is just the first day of another 365-day journey around the sun. Enjoy the trip. *HAPPY BIRTHDAY*_ 🍻🍻🍻 🎂🎂🎂 *ONCE AGAIN..HAPPY BIRTHDAY* H A A S T S A K N 💃💃💃💃💃 *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *2⃣7⃣* *G*idansu KHALEEL ya yanke shawarar zuwa danko baya tunanin a yanzun yasan abunda ya kamata ya aikata... Driving kawai yake ba dan yana da nutsuwar da zai iya kai kansaba,ikon Allah ne kad'ai ya kaishi,idanunsa sun koma jaa yayin da ta tsakiya har wani layi² yayi na coffee.... Shigansa harabar gidan bayan yayi parking ya nufi hanyan parlor,ta balcony ya hangosa zai shiga parlor,da yake KHALEEL ba mutum ne mai rik'o ba,shi kamar UMMIN sa yake,suna da sanyin hali... ''MAN!''....... Ya fad'a da d'an k'arfi ta yadda BB en yajiyo shi,d'an waiwayawa yayi ya kalli gurin da yaji maganar,inda yake ya nufa fuskarsa babu annuri a tare da ita... Chairs en da ke gurin ya zauna yana mik'a masa hannu,duk wani motsinsa idanun KHALEEL na kansa,ganin yadda ya chanja ya koma wani silent duk da dama bai da yawan magana... ''MAN lafiya kake kuwa?" Kallonsa kawai yayi da rinannun idanunsa... Sam KHALEEL bai kula da yadda idanunsa suke ba,sai yanzun da ya d'ago... Cikin tashin hankali KHALEEL ke tambayar BB ''MAN dan Allah ka fad'amin abunda ke faruwa,kaga kuwa yadda ka koma wani abun tsoro.......Dan Allah ka sanarmin abunda yake faruwa,ni kaina hankalina ya gaza kwanciya'' Hawayen da suka fara sauka kan fuskar BB masu matuk'ar k'una su suka dad'a sawa hankalin KHALEEL ya kai mak'ura wajen tashi,zuba masa ido kawai KHALEEL yayi,sai dai sam shi kansa hankalinsa baya tare da shi,ga shi BB en ya kasa masa magana bare ya gano dalilin damuwar tasa..... 《《》》 ''Dan Allah d'an uwa nan a ina nake?'' Kallonta yayi yadda take magana baiyi tunanin irin yaren da zai fito daga bakinta ba kenan,daurewa yayi ya bata amsa,yayin da yake k'are mata kallo from head to toe,hawaye ne suka sake b'alle mata,nan ko yaci gaba da kallon ikon Allah,shi dai bai san dalilin kukan ba bare ya bata baki tayi shiru,haka ya ci gaba da kallon ikon Allah har sai da tayi mai isarta sannan tayi shiru.... Tsab'an kukan da tayi muryanta har ya shige cike baka jin sautin muryanta idan tana magana har sai ka kalli yadda lips enta ke motsi.... Tunanin inda ya kamata ta nufa yanzun take,nan zuciyoyinta suka shiga fafatawa gurin ganin sun bata shawara... ''Shin gidanmu ya kamata na nufa ko kuwa?'' Take wata zuciyar ta sake bata shawaran ''A'a kawai ki koma gidan BABA MA'U'' Ta yi zurfi cikin tunaninta,har lokacin kuma ta kasa samun matsaya guda d'aya,duka kuma ta kasa yin na'am da shawarwarin da zuciyoyintan ke bata... Tana zaune tana ta kallon jama'a dake ta faman hada-hadar kasuwancinsu,yayin da yara suka sata gaba da ihun ga balarabiya,wasu suce y'ar india ce,da k'yar wanan mutumin ya kore su suka bar gurin.... ''Dan Allah MALAM a ina zan samu motan da zai kaini''...... Sai kuma ta d'an karkatar da kai gefe alamar tunani.... 《《》》 ''A kwai matsala MAN,ban san ya zan billowa al'amarin ba'' Shiru ya d'an yi ya kasa ci gaba da magana sai iska da yake furzarwa,wacce take fitowa cike da hucin zafi.. ''Wace irin matsala ne wannan?ni kam duk ka d'agamin hankali,kai kana cikin damuwa,nima ina cikin damuwa.....Buh...Ka k'i sanarmin abunda yake faruwa''.... ''Sun sa...ce......ta'' Abunda ya iya furtawa kenan,ko shima sai da yayi kokawa da kalmomin kafin suka bayyana,ta yadda za a gane.... Ido KHALEEL ya fiddo waje ''Wa aka sace? ZUHRA?ko wa???'' Kai ya shiga kad'awa cike da takaici baya ga k'uncin da yake ziyartarsa,zuciyarsa ta gama yin duhu,a iya wannan lokaci baya gane komai..... ''Uhmm!ita suka sace'' Ya sake maimaitawa,shikam KHALEEL ya kasa fuskantar wa ake nufi ''Dan Allah kamin bayanin da zan gane sosai.....Wace ce aka sace?.......Na tambayeka ZUHRA ka ce a'a,wace to daga cikin y'an gidan'' A tak'aice ya furta ''Wannan YARINYAR'' Fad'in hakan da yayi shi yasa ya fuskanci inda zancen ya dosa,take ko ya mik'e tsaye yana maimaita ''HASBUNALLAHU WA-NI'IMAL WAKEEL!!'' Da k'yar ya iya samun guri ya zauna,sun d'auki tsawon lokaci babu wanda ya iya magana cikinsu...... Ransa a b'ace yake fad'in ''Tabbas duk wanda yayi wannan d'anyan aikin,wallahi imaninsa ragagge ne,sam basu da tausayi bare imani....Laifin me ta aikata musu da zasu aikata mata wannan d'anyen hukuncin.....Baiwar Allah babu ruwanta......Wanda duk yake da hannu kan wannan aikin ya cancanci hukunci mai tsaurii'' BB kam ya kasa magana,har KHALEEL ya gama surutansa baibi ta kansa ba,tunani yake sonyi amma sam k'wak'walwarsa ta k'i karb'an ko wane irin hayaniya... Kafad'ansa ya kalla jin an dafa shi,hannun KHALEEL yabi da kallo,lokaci guda shi kansa KHALEEL en har ya sauya kamanni... ''MAN tashi muje'' ''Ina kuma zamu?'' Da k'yar BB ke tambaya ''MALAM kawai ka tashi muje,wannan lokacin bana tunani bane bare b'atawa'' Ganin BB en yak'i motsi yasa KHALEEL bugun shoulder ensa yana fad'in ''Ka tashi mu wuce'' K'in tashi yayi,wanda hakan da yayi ya k'ara fusata KHALEEL en ''Kada Allah ya sa ka taso en,wannan damuwar da kake nunawa duk na banza ne''... Bai samu daman k'arasawa ba saboda wani banzan kallo da BB ya wurga masa cikin matsanancin fushi ya mik'e ''Me ka sani game da al'amarina da ita da har za ka fad'i haka?Wannan damuwar da nake nunawa duk na banza ne ko ba haka ka fad'a ba?'' Wani murmushi yayi wanda da gani kasan sam bai dace da lokacin da aka yishiba.... ''Yeahhh! na fad'a idan da ace ka damu ya kamata ka biyoni muje'' ''Baza ka tab'a fuskata ba'' BB ya fad'a yana girgiza kansa.... 《《》》 'Bangaren MA'U kam zuwa yanzun duniya sabuwa,al'amura sai dad'a ta'azzara suke,neman maza yanzun ya zame mata jinin jikinta,duk inda take suna manne da farkokintan,babu gida babu waje yanzun har ta kai ga takan kulle gidan tayi ficewarta sai ta yini bata gidan.... Idan ta dawo kuma to za a tarar da ita da wani suka dawo bata tab'a iya kwana ita d'aya... Duk ko ranar da duniyancintan ya motsa ranar ba zaka tarar da ita gidaba gaba d'aya k'arshe a hotel zata kwana,koma ta shafe tsawon kwanaki kamar dai wacce tayi tafiya ganin gida..... 《《》》 ''Unguwan Miltara ko Rijiyan lemo......Wanne ne ma a ciki?'' Tama kanta tambayan,tana ta faman son ta tuna,idanunta sun koma ciki,duk kuwa da yanda KHUBRA ke da yalwar idanu... ''HAJIYA na ga kin kasa tunawa,me zai hana muje gidana'' Ya fad'a yana kallonta,yana kuma kallon abunda ke rungume jikinta,d'an kallonsa tayi da jan fuskanta,ita dai haka kawai taji ta aminta da shi,amma kuma taya za ta amince,ta sani ko bashi da aure,haka kawai ya kaita gidansa alhalin bashi da aure... Shiru tayi bata ce komaiba,shi kuwa sai kallonta yake da k'unshin bak'in ledanta dake rungume jikinta har lokacin... Kamar ya san abunda take tunani akai aiko ya shiga fad'in ''Ki yarda muje babu abunda zai faru dake yanzun haka y'ay'ana hud'u da mata ta'' Jin haka yasa ta mik'e ba tare da tunanin komaiba tana fad'in ''Muje to na gode sosai Allah ya saka maka da mafificin alkhairi'' Y'ar dariya yayi ba tare da ya amsa ba,ya shiga tura kurar ruwansa ita kuma tana biye da bayansa,suna tafiya babu wanda ya kuma tankawa wani a cikinsu..... 《《》》 Car keys ensa ya fizga kan mini table dake gurin,sai huci yake yayi gaba,da d'an gudu KHALEEL ya biyo bayansa,yana zuwa saitinsa ya fizge keys en yayi saurin bud'e driver seat yayi starting motan... Kallon mamaki BB yayi masa kafin ya zagaya ta d'ayan side en yana mai rufewa..... A 360 suka bar gidan,basu tsaya ko ina ba sai police station,office en DPO aka shigar dasu da yake yasan ABBAN KHALEEL,shi ya bada report en b'atan KHUBRA wani sergent dake gefe yana nad'ar bayanin.. Kasancewar ba komai ya sani game da b'atan nata ba,yasa ya dubi BB dake zaune ya dafe kansa ''Ka masa bayani kasan ba komai na sani game da case enba'' DPO ne ya kallesu su duka biyun ganin irin yanayin fuskokinsu da abunda yake d'auke akansu ya tabbatar suna cikin damuwa da b'atan yarinyar ''Ina ganin da kunzo da photonta da binciken zaifi zuwa da sauk'i'' Ya fad'a cike da alhini... KHALEEL ne ya bashi amsa da fad'in ''Gaskiya ABBA bana tunanin akwai photonta nan kusa'' ''To babu komai duk da haka in sha Allah gano inda take bazai yi wahala ba,Allah ya bayyanata''......... Kan BB ya juya yana fad'in ''Daurewa za kayi d'ana ka sanar damu abunda ya faru kaji,bayanin kane kad'ai zai taimaka mana ta hanyar gano inda take a halin yanzun'' Da k'yar ya iya tattara bayanan ya sanar da shi DPO yana zaune yana saurarensu har suka gama,sergent en ya fice... Godiya suka masa had'e da sallama suka fice jiki a sanyaye..... 《《》》 Gefen LADIYO itama ba'a barta a baya ba,zuwa wannan lokaci kam mu'amalarta da bokan nasu abun duk ya isheta kawai dai dan bata da yadda za tayi ne shi yasa ta zuba ido.. Da ta kaiwa TABAWA kukanta ko dariya tasata a gaba tana yi cikin muryan da yake nuna jin dad'i take fad'in ''Ke kam LADIYO ban san lokacin da zaki waye ba,shi MALAM BUBAN kashe miki k'ishirwa yake?ina ganinma kam kafin ki samu kansa ae sai da aka miki taimako......Yawwa kwana biyu babu labari ya ake cikima kuwa baki zomin da labariba'' Kai LADIYO ta yasar gefe tana fad'in ''Kayya dai kam TABAWA abun ba a cewa komai,dan lamura sai dad'a tab'arb'arewa suke,ni kam ina ganin hak'ura zanyi kawai.....Tunda na samu an rabashi da zancen wannan shegiyar y'ar tasa hakama ya isheni kam'' ''Aike kam dama wollahi kina da damuwa,banda abunki kin tab'a ganin an hak'ura da neman mafita,matsalarki kenan gidadanci'' (A raina nace duk uwar d'arin ce ae)....... Hud'uba iri daban-daban haka ta ci gaba da cusawa LADIYON munanan d'abi'u,wanda kafin ta bar gidan sai da ta kwashi kaso mafi yawa cikin abunda TABAWAN ta sanar da ita...... 《《》》 Tun da ZUHRA ta shige bedroom enta da plate a hannunta ta kulle k'ofan.Plate en ta tusa a gaba sai juya indomein take ta kasa kai ko da one spoon bakinta,hawaye ne ya ci gaba da saukowa kan face enta,damuwa duk ya mata yawa ga ba mataimaki sai Allah... Yini tayi a bedroom en ta kasa fitowa da k'yar ta rarrashi kanta ta soma cin abincin nata da yayi sanyi,spoon biyar ta iya ci ta ture plate en gefe,tunani duk ya dameta... ''Me yasa MAMA zata aikata haka?........Sam banyi tunanin da sa hannun MAMA ciki ba....Amma me yasa?'' Haka ta yini cikin d'akin dan kam itama bata jin za ta iya fita bare har ta samu damar hira da wani.... 'Bangaren MAMA da y'an fadarta ko damuwarsu bai wuce rashin abincin break da suka saba da cin mai kyau a kowane lokaci ba,sai dai wannan ranar ta zo musu da sauyi,ta yanda sun tashi cikin k'oshin lafiya sai dai babu garar da suka saba da ita kullum rana.... Yinin ranar haka suka wuni cin cornflakes,MAMA kam sam bata da kwanciyar hankali ta b'angaren girki coz ita sam bata jurar yin girki ko da sau d'aya a yini,shi yasa ma ta k'ule a d'aki ta gagara fitowa,su kuma yarantan ba shiga kitchen suke ba bare su iya yi da kansu... A wani gefen kam tana jin alhini na rasa KHUBRA a matsayin housemaid da tayi sa'a kaf cikin y'an aikin da sukayi a gidan.... (Ni ko nace kad'anma kika gani,ai yanzun aka fara)......... 《《》》 Binsa kawai take suna tafiya yana tura kurar ruwansa sai da sukayi nisa da cikin jama'a dan har sun fara shiga cikin gonaki dake bayan garin.... Da k'yar take tafiyan saboda gajiya da tayi,d'an tsayawa tayi tana hutawa har yayi gaba bai san ta tsayaba,waiwayowa yayi ya ganota can baya,kuran ya bari a gurin ya dawo baya... ''Yi hak'uri kinji mun kusa tarar da gidan'' Murmushi tayi tana kallon gurin,ita kam sam bata hango gidaba a gabanta,gudun kada ta masa wuk'anci a matsayinsa na wanda yake shirin taimakonta yasa ta daure ta ci gaba da binsa... Ci gaba sukayi da tafiya har suka tarar da inda ya ajiye kuran,suna tafiya yana juyawa baya,ganin babu mutane a gurin ko kad'an ya fakaici idon KHUBRAN d'an sakin kuran yayi ya sunkuya yana dafe cikinsa,a d'an tsorace ta matso gaba kad'an gareshi tana fad'in ''Lafiya k'alau kuwa kake,me yake damunka?'' Damuwa sosai ta bayyana akan fuskanta har tana neman mantawa da nata damuwan.... Sai da ta gama sakewa tukun ya fizge ledan hannunta take ko ya shek'a a guje ya nausa cikin jejin dake gaba kad'an da su.................. ~Kuyi hak'uri da jina shiru kwana biyu,bana jin dad'ine dats y baku ga posting ena ba,,,,,,, _1 luv my peps._~ *_~TEAM KHUBRA~_* *_REAL SMASHER_* 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *16/ʍɑվ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_* _ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._ *~________________________~* _Ga ubuk'atar kasancewa da group na *Y'AR GARUWA* za ku iya yin joining ta hanyar amfani da wannan link en..._ 👇 Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/EvdAvnFbBaX2BBMAwCCH4E *~________________________~* _MASOYA INA MAI BAKU HAK'URI,SAKAMAKON DAKATAR DA POSTING DA ZANYI,BISA GA GABATOWAR WATAN *RAMADHAN* IN SHA ALLAH,SAI MUN HA'DU BAYAN SALLAH DA YARDAR ALLAH,IDAN ALLAH YA ARA MANA LOKACIN,INA MUKU FATAN ALKHAIRI,DA FATAN UBANGIJI YA KARB'I IBADUNMU WANDA MUKAYI DA WANDA ZA MUYI,ALLAH YA DATAR DAMU,YA SANYAMU CIKIN BAYINSA Y'ANTATTU..._ 🌙⭐ *HAPPY RAMADHAN IN ADVANCE.* 🌙⭐ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *2⃣8⃣* *T*saye tayi tana kallon yadda yake gudu,k'afafunsa uwa robber band wajen talewa da suke kan tsabar gudun da yake,abunka da mara gaskiya akace ~{ko a ruwa gumi yake}~ ..... Ta rasama me ya kama tayi ita dai sai kallonsa take duk da yayi mata nisa.... ''KHUBRA ya kamata kiyi wani abu ko dan ceton rayuwarki'' Wata zuciyar ta kawo mata d'auki da shawara.. ''To ni me zan iya yi yanzun?'' Ta tambayi kanta tana mai ci gaba da tsaiwa ba tare da ta iya yanke hukuncin aikata komaiba,a hankali ta sulale ta zauna tsakanin kunya² dake gurin,da hannu biyu ta buga tagumi ta rasa meke damunta... Tana nan zaune har ya b'acewa ganinta,ajiyan heart ta shiga saki masu matuk'ar k'arfi kan kukan da ta shak'a a yau.... Rana ta dad'a yin zawali,a b'angaren KHUBRA sam zafin ranar bai ko damunta,dan kanta ta mik'e lokacin da ta gaji da zaman gurin baya ga yunwa da ta fara damunta.... Kuran da ya bari gurin shi zuciyarta ta gama bata shawaran ta tura,ta wannan hanyar ne kad'ai zata iya samun abunda za taci,cikin duniyar nan ba kowa ke iya taimakon wani ba..... Pushing enta ta shiga k'ok'arin yi sai dai ko kad'an kuran bai motsa daga inda yake ba,iya k'arfinta tasa ta shiga dannawa amma ina abun ya gagareta,haka ta zube gurin ta sake sakin wani marayan kuka,wanda baka iya jin sauti sosai cikinsa..... 《《》》 Tunda suka baro police station en babu wanda ya iya kula wani tafiyan kurame suke,babu d'aya da ya tankawa d'ayan.... Dai² gate ensu ya perker,fita yayi sai da ya zo center ensa kafin ya bud'e baki da k'yar ''Sai mun yi waya'' Ya fad'a tare da juyawa ya shige gida... Tun fitar KHALEEL a motan ya kasa motsi,zama ya ci gaba da yi a motan,sai da ya shafe tsawon wani lokaci,kafin ya matsa zuwa driver seat,dan sam bai jin zai iya fitowa a motan sannan ya koma da k'afarsa.Ko da ya koma enma da k'yar iya starting motan yayi gaba..Yanayin da yake driving en kad'ai ya isa ya bayyana rashin energy a tare da shi,da haka ya lallab'a ya isa gida..... Shigan KHALEEL gida yana tafiya uwa kazan da k'wai ya fashewa a ciki haka ya shiga parlor... Kwanciya yayi idanunsa a rufe ya d'ora hannunsa a kan fuskansa,fitowar UMMI daga kitchen ta ganshi nan kwance,yanayin yanda yayi ya tabbatar mata d'an nata ba k'alau yake ba,k'arasowa tayi ta dafa kansa,da sauri kuwa ya bud'e idanunsa yana sakin ajiyan zuciya... Hakan da yayi ya dad'a tabbatar mata da zarginta ''SON lafiya kuwa kake? Na sha fad'a maka ka dena sa damuwa a ranka,saboda ba abunda take haifarwa sama da dana sani,baya ga ciwo da zai shigeka ba tare da yayi shawara da kaiba..... Har kullum ina maka nasiha da ka ci gaba da mik'a lamarinka zuwa ga mahaliccinka,shi ne zai maka maganin damuwarka,damuwa bata tab'a zama magani,sai dai ma ta zama silar k'aruwar matsaloli'' Hannayenta da ta dafa shi dasu ya rik'e sosai,uwa wanda ke tsoron za a rabasu ''Na gode sosai UMMINA da sani a hanya da kike,Allah ya miki sakamako da mafificin alkhairi'' ''Ameen MY SON,Allah ya maka albarka,ya karemin kai daga dukkan wata fitina ta zamani'' ''Ameen UMMINA'' Su duka sukama juna murmushi,mik'ewa tayi da niyyar barin gurin maganar KHALEEL ta dakatar da ita ''UMMI ki tayamu da addu'ah mu samu a gano inda take'' 'Dan waiwayowa tayi tana masa kallon rashin fahimta,tun kafin ta kai ga tambaya ya katse mata kalmomin dake shirin fitowa ''UMMI sun sace ta'' Cike da al-hini yayi maganar yana yada kai gefe... ''Ban fuskanci me kake son fad'a ba SON......... Wace ce aka sace kuma?'' Damuwa ta dad'a bayyana saman fuskarsa a hankali ya furta ''Wannan yarinyar ta gidansu KHALEED!'' ''Innalillahi wa-inna ilaihi raji'un'' Bakinta keta maimaitawa har sai da ta samu nutsuwa kafin wasu tambayoyin suka shiga tseren fitowa daga bakinta ''Yaushe?kuma a ina hakan ta faru? garin yaya?ita HAJIYA MURJA tana wane sakacin aka d'auke y'ar mutane?ko kuwa bata sani ba?'' Kallon UMMIN nasa ya shiga yi uwa wanda ya fara ganinta yau ''Wallahi UMMI abunda na manta ban tambayi KHALEED ba kenan...... Amma gaskiya UMMI ina zargin da sa hannun HAJIYANSA'' Ta gefe ya d'an kalleta yana mai rik'e bakinsa,tunawa da warning da tayi masa ''Amma kiyi hak'uri UMMI idan na fad'i abunda ba dai² ba'' Kai ta kad'a masa kafin cike da mamaki ta soma magana ''Tabbas ko ni da kaina jin wannan maganar yasamin zargin HAJIYA MURJA....Da gangan akayi......Ko tantama babu wannan aikin shiryashi akayi,akwai sa hannu cikinsa'' Shiru dukansu sukayi suna jinjina lamarin... ''Allah ya kyauta,Allah ka kare baiwarka a duk inda take'' Abunda ya iya fitowa daga bakinta kenan ta sake yin shiru tana jaddada al'amarin a zuciyarta.... 《《》》 ZUHRA ce ta fito da kumburarren fuskanta zata kitchen danko k'ishi ke damunta,ta fito da niyyan d'auko ruwa,dai² zata wuce ta k'ofan MAMA ta ji ana magana k'asa²,kunnenta ta d'ora jikin k'ofan take ko kalaman da ta jiyo suka sake firgitata.... ''Ehhh!ba damuwa HAJIYA LAURA ai kin gamamin komai da kika samomin mafita'' Dariya ta saki mai k'arfi kafin ta ci gaba ''Wallahi kuwa mun rabu da kaska.....Yo to ta inama za ayi wata Housemaid zata zo tana neman juyamin kai.......maza biyu lokaci guda fa duk sun haukace kanta,shi wancan da yafi kowa haukama harda turomin mahaifiyarsa bayan ga y'an mata nan ina da su bai zab'i kowacce ba sai ita........Uhmm!shi kuma KHALEED......Ai ki barni da su tunda yanzun munyi maganinsu.....Allah kuwa,to ameen...Sai kin jini'' Jin maganganun tayi suna mata yawo akai,kenan zarginta ya zama gaskiya kan MAMA,hawayene suka sake b'alle mata,dafe bakinta tayi tana jiyo maganar MAMA,daga jima ka san da kanta take ''Ya zama dole na raba gidan nan da duk wani abu da zai sake tunamin da ke...... Barima kiga na tashi kaf kayanki dake gidan nan k'onasu zanyi,mun dai rabu da kaska sai aje can a sha jinin wani'' Jin kalamanta na k'arshe yasa ZUHRA saurin mik'ewa hanyan fita daga parlor ta nufa tana tafe tana hard'ewa kamar za ta kifa,har ta fice daga parlorn... Kansa ya had'e da steering motan ya shiga tunanin da bai san me yake tunawa ba,tsawon mintuna arba'in yana cikin motan ba tare da ya iya fitowa ba,kuma har lokacin ya kasa kashe motan... Fitowan ZUHRA daga cikin parlor tana waigawa tana kallon hanya tamkar wacce wani abun tsoro ya biyo,shi kuma ya d'ago yana bud'e motan had'e da kashewa ya fice,tafiya yake jikinsa babu k'wari... Buge juna suka yi da sauri ta d'ago ba tare da iya yin maganaba ta d'aga masa hannunta alamar ban hak'uri,tayi gaba abunta,tana kuma ci gaba da waiwayen hanya.... Kallonta kawai yayi,yanayin da take ciki ya tabbatar masa akwai damuwa,har zai shiga parlor ya fasa a baya ya bi hanyan da ta bi,har k'ofan d'akin.. A ciki ya tsintota tana ta faman binciken kayan dake d'akin,da k'yar ta iya gano keys en d'akin,kayan ta shiga d'iba tana zubawa a closet dake had'e cikin wall en d'akin..... Yana tsaye bakin d'akin yana kallonta har ta kammala ta fito,da sauri ta maida k'ofan ta rufe had'e da danna mata key..... Sai da ta juyo zata bar gurin sannan ta ganshi tsaye ya hard'e hannayensa a chest yana kallonta... 《《》》 Sai da ta gama kukan sannan ta mik'e ta karkad'e kayanta da suka b'aci da k'asa,zuciyarta cike da kishin kanta da tausayin rayuwarta ta sake d'ora hannunta a kan marik'in kuran.... Dannawa ta shiga yi,duk k'ok'arinta bai wuce taga ta taimaki kanta ba,addu'ah ta soma duk wacce tazo bakinta yi take kan neman taimako daga mahalicci,cikin ikon Allah tana ta k'ok'arin turawa bakinta kuma bai fasa ambaton Allah ba,tafiya kuran ya soma ta juyo da akalar kuran zuwa garin da suka bari yanzun.... Da k'yar take iya turawa,fuskanta zuwa jikinta duk yayi gumi kan wahalar da tasha na turo kuran,idan ta gaji ta tsaya ta huta haka taita fama har ta fara shigowa cikin garin.... Jama'a sai kallonta suke da mamaki yayin da wasu ke binta,ita kam ko a jikinta,dan ta d'aura aniyar neman halak enta,sana'a babu fashi yanzun ta soma duk abunda mutane za suyi babu ruwanta,za ta toshe kunnenta daga tsaigumin su,haka taita turawa tana wucewa,line ta soma bi d'aya bayan d'aya,wani line en idan ta shiga za ta tarar da shi cike da mutane y'an gulma wad'anda labari ya iske,ba maza ba mata,hatta da k'ananan yara binta suke duk inda tayi,ita ko ko a jikinta.... Ganin wannan sabon al'amari yasa mutane siyan ruwan ga wand'an dama basuyi niyyaba duk dan su shaida labarin da ya iske su,duk gidan da suka siya dai kaga wasu daga cikin y'ay'ansu maza suna saukewa suna shiga da shi,idan sun juye su bata kud'inta da jarkanta,haka zata k'ara gaba su kuma su bita da idanu... Kafin wani lokaci babu komai cikin kuran nata duka ruwan an siye babu sauran,bakin wata bishiya ta zauna tana lissafa kud'in naira d'ari biyu #200 cif,hamdala tayiwa Allah kafin ta huta abunta,bakin kasuwa ta sake komawa ta nemi mai abinci a gurin,tunani ta tsaya yi to na nawama ya kamata ta siya ne? Ta d'an jima tana yanke shawara,kan ta bayar duka ko a'a..... Mik'awa tayi duka ba tare da ta tantance ko yayi yawa ko baiba... Mai abincin ce ta kalleta da alamar mamaki tana fad'in ''Ke ko y'ar nan me za kiyi da abinci har na d'ari biyu,ai yayi miki yawa,ungo wannan'' Ta mik'o mata d'ari da hamshin,d'an murmushin k'arfin hali tayi ta karb'a tana mata godiya... ''A robber zan zuba miki ko kuwa a leda?na ga kamar bak'uwace ke ko?'' 'Dan murmushin ta sake yi tana fad'in ''Eehh!ni bak'uwa ce'' ''Allah sarki ai na ga alama tun zuwanki gurin nan'' Bata kuma magana ba ta karb'i abincintan a gefe ta samu guri ta zauna,ko rabi bata iya cinyewa ba ta mik'e tana dawowa matar da robber enta da sauran abincin ciki,kallon mamaki tayi mata kafin ta iya tambayarta ''Me ya faru kika dawo da shi haka?'' ''Uhmm!babu komai wollah babata na k'oshi ne'' Kalmominta da ta kira matar da shi wato ''BABATA'' su suka sa matar yin k'wallar farin ciki,kasancewarta bata tab'a haihuwa ba,har Allah ya d'auki ran mijin nata,tun daga nan kuma bata kuma wani auren ba... Ganin matar na hawaye ya sanyayawa KHUBRA jiki,haka taita kallonta uwa wata doluwa.... ''Y'ar nan gidan wa kika zo a garin nan?'' Tambayar ta bawa KHUBRA mamaki,amma sai bata nuna ba ''Ban san kowa ba a garin nan,nima kawoni akayi nan'' Da mamaki matar ke kallon KHUBRAN tana fad'in ''Kawoki akayi kuma?'' Kai ta kad'a mata,mik'ewa tayi tana kad'e jikinta da niyyan barin gurin ''Yanzun ina kika nufa y'ata?'' ''Zan wuce ne'' 'Dan tunanin matar tayi da sauri kuma ta katse KHUBRA dake haramar barin gurin ''Y'ata idan za ki yarda kuma kin amince ba zan tab'a cutar da ke ba,kuma idan har kin d'aukeni uwa a gareki...... Zaki iya bina gidana mu zauna tare,kin ganni nan tsawon shekaru talatin da biyar da aurena Allah bai tab'a azurtani da d'aba,amma yau na farko kin kirani MAHAIFIYA wannan dalilin yasa naji ina k'aunarki,tabbas zan rik'eki a matsayin y'a,idan har kin amince''.... Ta k'arashe maganar ta tare da goge wani layin hawaye dake kan fuskanta.... 'Dan tak'aitaccen murmushin yak'e tayi,kafin zuciyarta ta tuna mata abunda aka mata yanxun da ko awanni biyar ba ayiba.... Da sauri kuma wata zuciyar ta bata amsa da cewa ''Haba KHUBRA duniyar nanfa ba duka aka zama d'ayaba,ya kamata ki tuna yadda rayuwar ki ta faro,wasu na sonki wasu na k'inki,kada kiyi saurin yanke hukunci,kiyi addu'ah dan shi ne gatanki a rayuwa a kuma duniyarki''...... Siririyar ajiyar zuciya tayi,kafin ta furta ''Na amince BABATA amma da sharad'i'' Matar tana murna ta kalleta ''Koma wane irin sharad'ine na yarje miki fad'i kome kike so in sha Allah bazan gazaba'' ''Dama ina so ne nace...... Baba don Allah kada ki hanani neman abunda zan rufawa kaina asiri,komai tsafta,k'azanta,k'ask'anci ko samu da sana'ar take d'auke da shi''.... Kallonta kawai matar tayi ''In sha Allah bazan hanaki ba..... Amma wace irin sana'a ce wannan?'' ''Ba wata sana'a bace illa *GARUWA.............''* A d'an tsorace ta kalli KHUBRAN,ita ko sai murmushi take abunta,da fuskanta da har yanzun tak'i komawa dai².... Gudun kada tayi magana akan sana'ar ta KHUBRAN tak'i amincewa da buk'atarta,yasa taja baki tayi shiru,tana nai fad'in ''To shi kenan Allah ya wuce mana gaba,yayi miki jagora'' KHUBRA ta amsa da ameen..... ''To yanzun dai da kin bari sai zuwa gobe ko dan mu tafi tare kinga kyaga gidan namu ko?'' Ta fad'a tana d'an murmushi,itama KHUBRAN murmushi tayi ta sake neman guri ta zauna,tana ta kallon mutane da keta zuwa siyan abinci,tana zaune har abincin ya k'are tas,tana kallo matar ta kammala had'a kayan al-majirai suka d'aukan mata kayan nan ta juyo tana kallon KHUBRA ''Taso mu tafi y'ata'' Babu musu ta shiga bin matar a baya suna tafe tana tura kuranta na ruwa har suka isko wani k'aramin gida,nan suka shiga suka nemi guri KHUBRA ta adana kuranta da niyyan gobe da wuri zata fita sana'anta..... 《《》》 Kallonta yayi duk ta wani birkice ''Me yake damunki SISNAH?'' Bata iya bashi amsaba,hannunsa kad'ai ta jaa zuwa guarding suna tafe tana waiwayawa tana kallon hanya,guri suka samu suka zauna sannan a d'an tsorace ta juyo ''YAYANAH wallahi ina jin tsoro kada wani abu ya samu KHUBRA......Duk abunda ya faru BB MAMA ta san komai kuma wollahi da hannuta komai da ya faru,MAMA ce sila......Dan Allah YAYANAH ka nemomin ita pleasee'' Ta k'arasa tana rintse idanunta.... Tashin hankalinsa k'aruwa yayi jin ta ambaci MAMA,amma ya akayi tasan da sa hannun MAMAN a ciki?Yama kansa tambayan..... ''Me yasa kikace da sa hannun MAMA?'' Ya mata tambaya yana mai jin fad'uwar gaba,dan bai san wane amsane zai fito daga bakintaba ''YAYA Allah ina jin tsoro sosai.....YAYA yanzun na fito naji tana waya,amma bansan da wa suke magananba....Wallahi YAYA ita tasa aka sace KHUBRA'' Shiru yayi ya kasa magana kansa sai dad'a sarawa yake kan ciwon da yake masa vains en kansa duk sun gama bayyana a fili.... ''Kuma YAYA ko ta ce sai ta k'ona duk wani abu da ya shafi KHUBRA shi yasa na rufe d'akintan......YAYA ansa key en ka adana ni kasan MAMA zata iya buguna amma dan Allah kada ka bari ta sani kaji BB nah'' Ta fad'a tana d'ora masa key en a hannunsa,da sauri ta mik'e ta bar gurin tana had'awa da gudu,har ta shige bed room enta basu had'u da kowaba,da sauri ta maida k'ofan ta rufe..... A hankali ya mik'e yana tafiya,har bakin k'ofan bedroom en,key en ya sanya ya bud'e yana shiga ya maida k'ofan ya rufe yana mai locking enta ta ciki..... Kan katifanta ya kwanta yana sauke ajiyan zuciya,yanayin d'akin kad'ai ya bashi nutsuwa ko ba komai k'amshinta da yayi remaiming ciki ya kwantar masa da hankali,yana haka wani bacci mai dad'i wanda ta jima rabon da yayi shi ya d'auke shi..... 《《》》 Cikin d'aki matar ta mata iso tana mata shimfid'a,a hankali ta shiga ta zauna tana ta kallon ko ina na d'akin,zama matar tayi tana fad'in ''Ohhhh!niko ko sunanki ban tambaya ba,ina can d'okin tahowa da ke'' A hankali ta furta ''Suna na KHUBRA'' ''Allah sarki ni kinga suna na ZUWAIRA'' 'Dan murmushi kawai KHUBRAN tayi sai dai tambayan matar ya sa fuskarta saurin rikid'ewa zuwa tsantsar tashin hankalii.......... *~#KEEP FOLLOWING FAN'S....~* *Mu tara bayan sallah da yardar Allah,da fatan Allah ya karb'i ibadunmu,na barku lafiya,Allah ya sada mu da alkhairinsa....Ameen thumma ameen.* *~UR'S & ONLY~* *_REAL SMASHER._* 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *19/ʝųŋɛ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* _Ina taya d'aukacin al'ummar musulmi na duniya murnan sallah da fatan ubangiji ya amshi ibadunmu ya kuma sanyamu cikin y'antattun bayinsa.....ameen._ 👏👏 *HAPPY EID-EL-FI'DR.* *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *2⃣9⃣* *"O* ohh! Ni ko na miki wata tambaya d'azun sai dai amsan da kika bani ya tsayamin a rai,na kasa fuskantar abunda kike nufi "... 'Dan d'agowa tayi tana kallon matar saboda rashin fuskantar maganar ta new mother en nata.. Gane hakan da tayi shi yasa tayi d'an murmushin yak'e kafin ta furta "A d'azun na miki tambaya kan gurin wa kika zo a garin nan,sai dai amsan da kika bani yasa nake son sanin me yasa aka sato ki kuma wane azzalumi ne ya aikata miki haka?" Fuskanta cike da tashin hankali haka ta sunkuyar da kai k'asa,dan kam ta tabbata mai afkuwa na shirin faruwa,tunda matar ta soma tambayanta lallaine a k'arshe matar ta koretama gaba d'aya,wannan tunanin shi yasa ta dad'a sunkuyar da kanta k'asa gudun kada matar ta gane k'aryan da take shirin yankowa bata iya d'agowa ba,idanuntan nan sun dad'a fitowa kan tsoro da ya cika zuciyanta,duk da dai tasan ba wai laifinta ne yasa aka aikata mata hakanba... Tana nan zaune tayi shiru amsa tambayan ya gagareta tana ta taradaddin sanar da BABA ZUWAIRA,ta tsinkayo muryanta tana fad'in "Niko KHUBRA idan babu damuwa zan so sanin daga wane gari kika fito da kuma asalinki?" Jin wannan tambayan yasa ta sauke ajiyan zuciya a tunaninta ta tsira daga wancan tambayan,shi yasama cikin k'warin gwuiwa ta bata amsan "Daga KANO nake,BABATA dan Allah nan wane gari ne? ban san ina ne nan ba" KHUBRA ta fad'a yayin da wasu hawaye masu d'umi suka fara sakko mata,gefen hijab na jikinta ta kama tana gogewa,duk wani motsinta idon matar na kanta tana binta da kallon tausayi... "Allah sarki nanma duk cikin kano kike ae sai dai nan muna daf da jihar jigawa,sunan wannan garin ZAKIRAI,amma cikin kano wani gari kike?" Raba ido ta hau yi tana son tuno sunan unguwan da suke,tunani take ko zata iya tuno sunan unguwan da suke,amma ta kasa..... Katseta BABA ZUWAIRA tayi da wata tambayan "Ke kuwa mene ne ya faru dake da har wasu suka satoki daga gidanku kuma hannun iyayeki zuwa wannan gari,kuma me kika aikata musu da zafi har haka?" Kukanta tayi k'ok'arin had'iyewa,kafin cikin nutsuwarta ta soma da fad'in "Dan Allah MAMA kiyi hak'uri kuma ki yarda da ni,ko da na fad'a miki gaskiya baza ki koreni ba"... 'Dan tsagaitawa tayi ta d'ago kanta tana kallon new mother enta BABA ZUWAIRA.. Kai ta soma kad'a mata kafin ta bud'e baki cikn sanyin jiki ta furta "In sha Allah babu abunda zai faru,ke dai ina son ki fad'amin gaskiyarki,dan da ganinki bana tsammanin k'arya daga gareki,ina fatan kuma zaki d'aukeni matsayin mahaifiya ki sanar da ni komai".. "In sha Allah" KHUBRA ta fad'a a zahiri,yayin da can k'asan zuciyarta take fad'in "kiyimin afuwa amma kam tabbas bazan iya sanar dake *SIRRIN RAYUWATA* ba",in sha Allah dana fad'a dama sai Allah ya baka iko,kuma k'arya wajen kare kai ta halatta,tana kaiwa nan ta datse tunanin had'e da sauke wata nannauyar ajiyar zuciya... "Kamar yadda na sanar miki ni sunana KHADIJA amma mahaifina na kirana da KHUBRA,saboda kasancewar sunan mahaifiyarsa gare ni wannan dalilin yasa mutanema ke kirana da KHUBRA kamar yadda mahaifina ke kirana,mahaifiyata Allah yayi mata rasuwa tun ina jaririya" Daga nan ta shiga bata labarin irin zamanta a gidansu ZUHRA,sai dai ta b'oye alak'arta da gidan da kuma irin zaman da take,hakama alak'arta da MA'U,LADIYO da ma k'auyensu,abunda ta iya sanar mata kad'ai kishiyar mamanta ce take son ta auri k'aninta ita kuma bata so,kan wannan dalilin ta d'ora mata karan tsana,tun daga ranar take zuga mahaifinta,ganin yak'i amincewa ne yasa tasa aka satota daga gidan wanda k'arshe suka yasar da ita a bakin kasuwar garin nan..... Shiru tayi tana jan numfashi a hankali,kanta har lokacin yana k'asa saboda tunaninta tana d'agowa suka had'a ido matar zata gane k'arya ta mata.. "Allah sarki y'ata,in sha Allah da sannu duk mai hannu a ciki sai ya ga sakamako,amma mai zai hana na d'oraki a hanya ki koma gida,saboda kinga baki san halin da mahaifinki yake ciki ba"..... Cikin sauri KHUBRA ta katseta da muryar tausayi, "dan Allah BABATA kiyi hak'uri kada kuma ki ce nak'i bin shawararki,wallahi ina son sanin halin da mahaifina yake ciki,amma ina tsoron zuwa gida saboda ban san me zan je na tarar ba,ki kyale ni na zauna tare da ke har zuwa wani d'an lokaci,in sha Allah da kaina zan miki maganar tafiyata idan lokaci yayi" ta k'arasa tana goge fuskarta da hijab enta... Yanayin yadda tayi maganar shi ya sanyayawa matar jiki,tausayin KHUBRAN duk ya lullub'e mata zuciya haka take ta bin KHUBRAN da kallon tausayi.. "Shi kenan babu komai KHUBRATA in Allah ya yarda zaki ci gaba da zama a nan,Allah yasa hakan ya zama alkhairi a garemu baki d'aya" Tako amsa da ameen,wani sashe na zuciyanta yana farin ciki da amincewar da matar tayi.... 《《》》 Daf da za a shiga masallaci ya farka har an idar da kiran sallan maghreb,da sauri ya mik'e ganin garin yayi duhu,agogon dake d'akin ya kalla,da mamaki a kan fuskansa cikin rashin gasgatawa ya nufi window yana mai d'aga cottains en aiko take ya gasgata abunda ya gani danko rana ta jima da fad'uwa,da sauri ya juya ya shige toilet en d'akin.... Cikin sauri ya idar da alwalan lokacin har an tayar da sallah a nan saman carfet ya kabbara sallah da yake yana iya jiyo masallacin kuma gudun kada ya rasa jam'i kafin ya fita... After ya idar yayi nafila,nan ya zauna yana addu'ah.. Ko da ya idarma kasa fita yayi ya kishingid'a jikin katifan yana tunanin baccin da yayi cikin d'akin,yayi nisa cikin tunani ya jiyo ana jijjiga k'ofan a d'an zafafe ya mik'e saboda yadda ake bugun k'ofan kamar za a karyata,shifa yanzun baya son damuwa kamar yadda yake jin haushin kowa a gidan idan aka d'auke ZUHRA da damuwarsu take kusan iri d'aya... Key en yasa ya bud'e k'ofan kamar an cillota ta shiga k'ok'ari fad'owa kansa cikin sauri ya kauce ta hanyar ja baya kad'an a kan hanyan,Allah ya taimaketa ta rik'e k'ofan bata kai ga fad'uwa k'asa ba,ganin tana k'ok'arin shigowa yasa ya tare hanyan,ta hanyar tsaiwa tsakiya... 'Dagowa tayi cikin fushi ta furta "KHALEED yaushe na fara wasa da kai da zaka tsayamin a hanya?.........Ammm!mene ma ya kawoka d'akin nan tukuna kana neman wani abune ciki?" Kamar an dasa gini haka ya mata ko "A" bai furta mata ba,kuma yak'i barin gurin... Hannunsa ta kamo da niyyar janyeshi daga gurin saboda a tunaninta zata iya,sai dai ko gizau baiba,ganin ta kasa yasa shi sakin wani murmushin yak'e mai sauti da yasata kallonsa.... Had'e fuska tayi alaman babu wasa.. "KHALEED kaa matsa a nan ko kuwa sai ranka ya b'aci dan yanzun zan baka mamaki?" "Uhhhmmm!MAMA ai an gama bani mamaki duk duniya,abunda kika aikatama kad'ai ya isa ya gama bani mamaki,amma MAMA ki tuna idan kin aikata haka akan y'ar wani shin bakya tunanin naki y'ay'an? idan Allah ya tashi kamaki me zaki fad'a masa lokacin da kika tsinci kanki a gabansa a lokacin da kowacce gab'a ta jikinki sai ta bada shaida akan abunda ta aikata,MAMA ki tuna da lahirarki sannan ki tuna irin tanadin da kika yi mata''....... "Kaiiiiiiiiii! dakata ni sa'arka ce da zakamin wa'azi?kada ka manta ni na haifeka ba kai ka haifeniba da zaka tsaya kana fad'an maganar da ranka yaso,kuma yanzun maza ka kauce ka bani hanya"..... Cikin tsawa da fusata take magana tana jifansa da wasu mugayen harara.... 'Dan murmushi ya sake yi mai ciwo yana kallonta,shi kam yau yaga ikon Allah,gaskiyan ne bata so a fad'a mata kenan?....... "Shi kenan MAMA duk abunda kikayi dai² ne,amma ki sani nasan duk wani shirinki akan KHUBRA da kika sa aka d'auke,sai dai hanzari ba guduba duk wani yunk'uri da za kiyi idanun jami'an tsaro na kanki,saboda haka babu laifi kiyi duk abunda kike ganin ya kamata"...... Mari ta d'aukeshi da shi da yayi saurin sashi yin shiru yana dafe da gefen fuskansa da ido ya bita,lokacin ita kuma ta juya ta bar gurin cikin sauri..... Wani murmushin ya sake yi,kafin ya juya ya kulle k'ofan yana mai barin gurin shima,zuciyansa duk ta cushe da tunani.... 《《》》 "Amma kuwa wollahi za muyita dan wollahi sai anji kanmu da MA'U a yau kam,dan ta raina ni ta kama hanya ta bar garin nan da yarinya lokaci mai tsayi amma ko kobo bata tab'a kawomin ba,tabbas kam sai nayi maganinta"..... Ita kad'ai zaune sai surutai take kamar wacce ta zautu,duk ta dad'a ramewa ga wani tsufa da ta dad'a yi kamaninta sun d'an jirkita.... Sallama akayi k'asa² daga bakin k'ofar shigowa gidan,hannunsa d'auke da robber 25 litres guda biyu dattijon ya shigo haka ya wuce ya juye ruwan cikin randunan dake jikin dangar kara ta gidan... "Wai tun d'azu daka fita sai yanzu ka dawo gaskiya anyi malalaci a nan" Ko juya ya kalleta baiba bare ya tanka mata,yana gama juye ruwan ya shige d'akinsa baiko bi ta kantaba..... "Bari dai kiga na mik'e ni inama zan samu aron tarho na kira wannan y'ar banzar na jita shiru,ga shi ni kuma ban san inda take ba a garin na kano" Tayi maganar lokacin da take k'ok'arin yafa mayafin hannunta da ya cukuikuye saboda daud'a da rashin guga,nan ta bazama tayi waje...... 《《》》 Shigansa bed room ya kwanta yana tunanin abunda ya kamata ya aikata,sam baya son a sake jefata wani halin duk da dai yanzunma bai san a wane yanayi take ba.... "Ya zama dole na nemo ki duk inda kika shiga a fad'in duniya.........Tabbas MAMA kin aikata kuskure mafi muni a rayuwa amma da sannu zaki girbi abunda kika shuka..... Wani tunani ne ya bijiro masa take ya mik'e yana laluban phone ensa,kaf d'akin ya duba bai gansuba,d'an tsayawa yayi yana tunani da sauri kuma ya fice daga room en,cikin sauri² ya kama hanyan fita.. A mota ya gano su,inda ya tarar da tarin miss-calls duk daga KHALEEL,kira yabi line en nasa da shi.... "Dallah MALAM ina ka shiga kasa sai nemanka nake tun d'azun?" "Sorry BRO na manta phone a mota.....Ammm a kwai maganar da nake so muyi,idan kana gida yanzun zan k'araso" "Ok ba damuwa sai ka k'araso" Sukayi sallama,motan ya bud'e cikin y'an mintuna ya bar gidan..... Bai wani b'ata lokaciba ya isa gidan,inda ya tarar da KHALEEL en a parlor,nan suka gaisa da UMMI tana zaune suna kallon AL-JAZEERA.... Ta saba duk lokacin da yazo zata tambayeshi mutanen gida amma yau kam suna gaisawa tayi shiru ta juya taci gaba da kallonta.... KHALEEL ya kalla yana fad'in "MAN muje ko?" Mik'ewa sukayi suka fice,yayin da UMMI ta rakasu da kallon tausayi.... A haraban gidan suka nemi guri suka zauna,nan kowa yayi shiru... KHALEEL ya kalleshi da mamaki "ya dai ka ce da magana kuma kayi shiru" "Wallahi ina jinjina maganar da zan fad'a ne kawai" "To Allah ya kyauta" "Ammmm!abu na farko dai da nake son sanar da kai yanzun,ina son mu koma gurin D.P.O da kai gobe,saboda ina son a bamu y'an sanda da zasu dinga kulamin da al'amuran MAMA" "MAMA kuma kan wane dalili?" KHALEEL yayi tambayan cikin hanzari... "EHHH!MAMA....." "K'wak'walwarka ta tab'u ne da zaka sa ayi mata haka ko kuwa ta aikata wani laifi ne?" "Uhhmmm!ni dai abunda nake so ayi kenan idan zaka to"..... "Kaga MALAM babu inda zani,ta inama zan biye maka mu aikata wannan shirmen" Cikin fushi KHALEED ya mik'e yana fad'in "Kada Allah yasa kayi en,dan ka nunamin haka bazan damuba saboda baka san dad'i ko ciwon k'anwa ba idan wani abu ya sameta saboda kai kad'ai ne,amma ka sani akan KHUBRA zan iya aikata komai...... MAMAN da kake maganar ba zaka bada goyon baya akanta ba,itace silar faruwar komai"..... "Meeeeee?kana nufin ita tasa aka sace KHUBRA ko me,ta yaya ka tabbatar da hakan?" "Ban saniba,idan ka d'auka wasa nake to ka daina,tabbaci nake baka kan MAMA tasan komai kuma ITA CE SILA"...... 《《》》 Washe gari da wuri KHUBRA ta shirya ta fita don yau kam sai ta dangana da rafi zata d'ebo ruwa,shi yasa tun kafin rana ta gama haske garin ta fice,inda tayi sallama da BABA ZUWAIRA sunama juna fatan sa'a.... Lokacin da BABA ZUWAIRA taga fitar KHUBRA binta tayi da kallon tausayi idanunta duk sun ciko da hawaye,fatan samun nasara tayi mata,tana jinjina al'amarin yarinyar,yarinya kyakyawa amma ana neman nakasta mata rayuwa,tabbas dan dai kada tayi magana ne kan wannan sana'ar ta KHUBRAN ta janyo abunda zaisa ta gudu daga hannunta amma kam tabbas da sai ta hanata dan sana'ar ba ta y'a mace bace,ko shi kansa d'a namijinma wannan sana'ar tayi wahala gareshi,sai dai dan kawai neman halak..... Cike da alhini ta kammala shirinta ta fice zuwa bakin kasuwa..... 《《》》 Tun bayan da MAMA tabar gurin da BB yake zuciyarta ta kasa samun nutsuwa jin ya ambaci police.. "Aiko ko ba don Allah ba na saurara hakanan tun kafin a kamani a gark'ama a jail" Tana gama maganar ta afka d'akin tana mai rufewa da key...... Niko nace *"KOWA YA TUBA DAN WUYA BA LADA"*...... *_~#TEAM KHUBRA~_* *_REAL SMASHER._* 💠?💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *21/ʝųŋɛ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* _Wannan shafi tukuicine gareku masoyana kuma masoyan wannan novel nawa na *Y'AR GARUWA* a duk inda kuke a fad'in duniya ina al'fahari daku,idan babu ku tabbas babu ni ina sonku so irin wanda bazai fad'uba da baki,Allah ya barmin ku a duk inda kuke....Na gaisheku oll 👌 kuyi komai ba komai *SMASHER* taku ce..._ _Fatan munyi sallah lafiya, ubangiji ya maimaita mana..Ameen.._ *~________________________~* _Sisinah wollah *GENTLE,SMASHER,HUBBEEY,LIPTON* tare da *AUFANA* muna matuk'ar alfahari dake wollai muna godiya da sadaukarwarki gare mu,jinjinar ban girma ga *CWEET DIDEEYLOV* Allah ya d'aukaka mana ke ki jima kiyi k'arko lokacinki ne yanzun ki ci gaba da haskawa cikin duniyar yanar gizo-gizo,muna nan biye dake duk inda kike...Godiya mai tarin yawa Allah ya k'ara miki lafiya da nisan kwana mai amfani.._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *3⃣0⃣* *Z* ama yayi kamar wanda aka dangwarar abun da yaji daga bakin KHALEED en duk ya d'aure masa kai,kallonsa ya sake yi yana son sake tabbatarwa dan kada suzo suyi abu da ka shi yasa a wannan lokacin da ya sake kallonsa ya furta "Da dai ka nemi guri ka zauna,dan ni har ga Allah ina buk'atar kamin k'arin bayani kada muzo muyi abunda zaisa muyi DANA SANI" Wani banzan kallo BB ya bishi da shi had'e da sakin tsaki,ba tare da ya zauna ba kamar yadda KHALEEL en ya buk'ata ya fara magana "Kafi kowa sanin halina kamar yadda kasan ba zan yi maka k'arya ba" "Hakane amma kasan shi al'amari irin wannan ba a masa gaggawa,da ka dakata munyi bincike tukuna" "Heeyy!MALAM har wani BINCIKE kake neman muyi bayan wanda nayi,ko an fad'a maka nima ina cikin mutanen da suke yanke hukunci cikin gaggawa? Idan mafarki kake to maza ka farka dan wannan kwana² da kakemin bazai hanani abunda nayi niyyaba"... "To Allah ya kyauta,kai matsalarka kana da shegen taurin kai,baza ka tsaya kayima mutane bayaniba sai dai ka bada magana a dunk'ule" "Kai kuma gaka mai kullallen kai da baka iya fuskanta ko?" "Mtssssss!Allah ya shirye ka,amma zauna muyi shawaran hanyan da ya kamata mubi kafin muje wajen D.P.O" Jin da yayi ya ambaci D.P.O shi ya bashi damar zama "To yanzun mene abun yi ne kam?" BB ya tambayi KHALEEL "Ummmm!ina ganin mu bari zuwa gobe sai muje mu sanar masa duk halin da ake ciki,ina tunanin haka ya kamata muyi" "Toh!hakanma yayi Allah ya kaimu.....Muje nama UMMI sallama zan wuce gida dare na dad'a yi" "Ok ba matsala muje" Mik'ewa sukayi suna masu nufan cikin gidan.... A parlor suka tarar da ita har time en tana kallo,sallama ya mata,ta bishi da fatan isa gida lafiya.. Har bakin motor KHALEEL ya rakashi sukayi sallama tare da musabiha,yayima motor en key........ 《《》》 'Daya bayan d'aya take bin robber's en nata tana zuba musu ruwa yayinda cikin k'arfin hali da k'arfin zuciya take d'auka tana jerasu cikin kuran nata,haka taita fama har ta gama jerasu.. Hannu ta mik'a saman pore head enta tana goge sweat da ya tsatsafo mata,sai da ta d'an huta tukun kafin ta kama hanyan shiga cikin gari,kamar jiya haka tayi ta zagaye cikin garin,kafin wucewar awa d'aya babu komai cikin kuran nata,kasancewar garin sun d'anyi nisa da gurin da ake d'ebo ruwan,shi yasa wasu daga cikin mutanen garin basa son zuwa d'iban ruwan,yayinda wasu kuma suka fi son *"Y'AN GARUWA"* su kawo su saya.... Ta bakin kasuwa ta biyo zata koma,a dai² lokacin BABA ZUWAIRA na kan ciniki itama,ta hango KHUBRA lokacin kuma rana har ta bud'e sosai,da murmushi a fuskanta ta k'araso... "Y'ata ta kaina da ganin wannan murmushin da kike akwai alamun nasara" BABA ZUWAIRA ta fad'a itama tana murmushin "Wollahi kuwa BABATA anyi nasara" "Aaa!masha Allah,maza zo kici abinci kafin ki tafi" "Laaa!BABA nafa ci abinci d'azu kuma ni bana jin yunwa yanzun" "To shi kenan maza zo ki huta kafin ki tafi ko" "A'a gara dai na koma bakin sana'a anjima sai na huta" "To shi kenan Allah ya bada sa'a" KHUBRA ta amsa da "ameen" sannan ta kama hanyan komawa rafi,kamar wancan lokacin haka ta kammala ta sake biyo hanyan jejin zuwa cikin gari...... 《《》》 "Haba HAJIYA LAURA nafa fad'a miki yanda al'amarin nan ya kasance,wallahi yaran nan yana neman ya jagulamin lissafi,gaba d'aya ya gama sanin duk wani abu dana aikata kan wannan matsiyaciyar yarinyar... 'Dazufa da yanamin magana kamar shi ya haifeni,har da yimin wani wa'azi" "Kai HAJIYA MURJA kina d'aukan komai da zafi,banda abunki dan yayi miki wannan maganar shi ne zai sa ki tashi hankali akan wannan maganar" "To me kike so ayi kina ganin yadda yake maganar police kinga kuwa shirinmu yana neman rushewa"...... "Ni kam dan Allah HAJIYA MURJA ki kwantar da hankalinki,zan san yadda zanyi na ganin babu abunda ya faru" "Uhmmm!HAJIYA LAURA kenan lallai baki san halin KHALEED ba,ko ni da nake matsayin mahaifiyarsa ina shayin shiga al'amuransa,saboda halinsa kaf irin na maifinsa ne,idan sukayi magana basa tab'a canzawa,suna da matuk'ar taurin kai,shi yasa nake jin tsoron su furta wata magana dan ina da tabbacin ba janyewa zai yiba".... "To ai shi kenan amma dai duk yanda ake cikima zan sanar miki" Ko sallama HAJIYA MURJA bata iya yiwa HAJIYA LAURA ba ta datse kiran,saboda hankalinta tashe yake da abunda yake shirin faruwa tsakaninta da KHALEED da yake neman tada mata K'AYAR BAYA... Kaiwa da kawowa ta shiga yi cikin d'akin,sam ta kasa tunani hankalinta sam ya kasa kwanciya..... 《《》》 "Ke dallah kefa nake jira kin wani kwanta kamar kayan wanki,bayan kin san ke nake jira,bana son wannan rainin wayon,kawai hajiya ki tashi ina son jina a sama cikin hazo ina yawo" Da kyar MA'U ta d'ago tana kallonsa "Haba mana kayi hak'uri zuwa anjima,ina jin bacci yanzun kome kake buk'ata idan na tashi kayi,amma yanzun ka kyaleni" "Ke ai kinji matsalarki da an tab'aki ki ambaci gajiya ko bacci" "To me kake so nayi maka idan ban hutaba so kake na mutu a tsaye ko da yaushe kana aiki a kaina sai kace wata engine" "Kai baki fahimceni bane,amma ai ba haka nake nufi ba,kin gane so nake ko da one round ne na k'ara kin gane ai" Cike da duniyanci yayi maganar yana mata winking... "Uhmmm!baka da dama idan kaso abu kamar d'a yaso fitowa daga cikin mahaifiyarsa,idan ban amince bama bazaka barni nayi bacci cikin kwanciyar hankali ba ya zanyi da kai" Dariya suka saka duka kafin su lula duniyar masha'a kamar yadda suka saba.... 《《》》 "Yawwa y'ata ta kaina gara da kika dawo kinga yamma tayi sosai dama kuma ke nake jiran ganin dawowarki maza yanzu mu wuce gida" "To BABA barin sa kayan a can" "Su kuma robobin ki kaisu ina?" "Laaaa!bari kiga yadda zanyi zasu shiga gaba d'aya" Da saurinta ta k'arasa bakin kuran robber's en ta hau d'ora wata kan wata a kwance,sannan ta shiga d'ora coolers a gurin data samar tana gamawa suka kama hanyar komawa gida,suna tafe kowa da tunanin da yake a zuciyarsa..... Duk inda suka gifta kaga mutane na k'usk'us akan neman sanin alak'ar dake tsakaninsu sai dai duk gulmar tasu babu wanda yasan gaskiyar al'amarin...... "Kai KHUBRA aikin nan yayi miki yawa ki bari muyi tare" "A'a wallahi BABA ki bari zanyi,yanzu zaki ga har na gama fa" "Kawai dai dan babu yadda zanyi shi yasa zan bar miki aikin nan,Allah yayi miki albarka" "Ameen ya Allah....Laaa!na manta BABA ban baki cinikin da nayi d'azuba" 'Dan murmushi BABA ZUWAIRA tayi bata ce komaiba,ta zauna cikin rumfa tana gyara kayan miyan da zatayi na abincin gobe.. Har ta gama wanke cooler's en ta kawo su cikin rumfa ta kife su duk dan ruwan ya fita daga ciki.. Kud'in ta fito da ta kawo shi gaban BABA ZUWAIRA ta ajiye,a hankali BABA ta d'ebi kud'in tana lissafawa,da murmushi a fuskanta ta kalli KHUBRA "Masha Allah,gaskiya kinyi ciniki sosai Allah ya k'ara bud'awa" Suka amsa da ameen... "Yawwa KHUBRA abunda nake so dake gobe idan Allah ya kaimu zan siyo miki banki na k'asa da zan na sa miki kud'in a ciki kema" Bata iya,magana ba sai murmushi da tayi,ita kam tana son matar ganin yadda ta d'auketa kamar ita ta haifeta,tana son matar saboda bata da hayaniya kamar sauran mutane........ 《《》》 Tun da sanyin safiya ya gama shirinsa cikin k'ananan kaya,fuskansa yayi wani fresh sai dai rashin fara'a kamar kowane lokaci ya fito,har ya kai bakin k'ofa akayi magana da yasa shi juyawa "YAYANAH barka da safiya" Fuskanta da fara'a take maganar a hankali ya d'anyi murmushi ta gefe a hankali cikin nutsuwa ya amsa mata... "YAYANAH fita za kayi da safen nan?" Da kai ya amsa mata yana juyawa yaci gaba da tafiya "Ammmm!BB da ka bari kaci wani abun kafin ka fita,na kammala dama yanzun nake shirin zuwa na kiraka muyi break" Tsayawa yayi a inda yake,kome ya tuna kuma ya dawo,d'an murmushi sukayi suka nufi dinning tare... "Woww!delicious CWEETY yaushe kika iya girki ne kam,nasan baku iya komai ba,ko dai wani yayi ba keba?" "Laaaa!BB Allah ni kam na iya babu wanda ya taimakamin da kaina nayi... Tun kafin kaci har ka fara santii" "A'a fa CWEETY ni kam babu wani santii da nake,kawai dai na fad'a ne" "Uhmm!to ai shi kenan idan ka ci sai kunnenka ya fice kan dad'i" "Aaaa!ai kuwa na fasa kada ina ci kunnena ya fice kiyiwa mai ni asara,maza kici abunki ke d'aya" Dariya sosai sukayi kamar ba sune suke cikin damuwa ba,sun maida damuwansu nasu su kad'ai yayinda akan fuskokinsu babu wani abu da ya wuce annuri duk dan kada kowa ya gane halin da suke ciki... Da kyar ta dawo dashi saboda mik'ewa yayi zai tafi,dariya suka sa dukansu,haka suke break da annashuwa.. "Amm!BB kace wani abu d'azun d'an dad'a maimaitawa naji" Kallonta yayi yana murmushi "Me na fad'a da kika manta" "Ba kace baza kaciba ko dan kada ko ayiwa wa asara?" Dariya sosai yayi saboda ya tuna me take nufin ya fad'a "Nak'i wayon na fad'a miki kiji ki dinga fad'awa saura......." "Laaaaaa!wallahi BB a'a nawa nakema da zan fara kula samari" "Yawwa CWEETY gara ki tsaya kiyi karatunki dama na fad'i hakane dan na tsokaneki" "To YAYANAH d'an fad'amin kaji" Ta marairaice fuska kamar za tayi kuka... Mik'ewa yayi ya soma tafiya,tana kallonsa har ya kai bakin k'ofan fita daga parlor sannan ya juyo yana murmushi "Mai ni nace" Yana fad'a ya fice da sauri har da dariya,nan ko ZUHRA ta zauna tana ta kwasar dariya,sai da tayi iya yinta sannan ta tsaigaita "BB nah kenan wai mai shi" Tana ta faman dariya ta ji maganar ASHNA "Ke kuma lafiyarki kike faman dariya kamar wata tab'ab'b'iya" "Ke dallah dakata,kuma daga yau duk ranar da kika sake cemin tab'ab'b'iya wallahi saina nuna miki tab'in hankali,banza kawai" "Dan uwarki dawa kike?" ASHNA ta tambaya tana nufo inda ZUHRA take "Dake nake sai me?" Kamata ASHNA tayi da kokawa nan ko ZUHRA ta shammaceta ta timata da k'asa ta shiga jibgarta baji bare gani,sai da taji dukan ya isheta gashi ta kasa ture ZUHRA daga kantane yasa ta fasa ihu wanda ya janyo hankalin MAMA da sauri ta fito tana fad'in "Me ya faru ne ASHNA kike mana ihu cikin gida da wannan safiyar?"....... Maganar ce ta mak'ale ganin ZUHRA a kan ASHNA tana jibga "Ke baki da hankali kike mata irin wannan dukan?bazaki d'aga taba sai na zo kanki?" Har ta k'araso gurin ZUHRA bata san me take cewa ba,fizgota tayi ta kifa mata mari wanda yasata sakin k'ara wadda tafi ta ASHNA.... Cikin sauri ya fad'o parlorn kamar an harbo shi yana raba eyes,ganin ZUHRA na kuka ya nufi inda take "Me ya sameki CWEETY?waye ya tab'aki?" "Ba MAMA bace ta mare ni akan waccan dak'ik'iyar" Wani mugun kallo ya jefesu da shi,kafin ya kama hannunta "Yi shiru kinji maza je d'auko vail enki mu tafi" Da gudunta ta bar parlorn,cikin sakanni ta dawo ya rik'e hannunta suka fice,MAMA da yar lelenta suka rakasu da harara.... A mota BB yake tambayan ZUHRA me ya had'asu da ASHNA,nan ta kwashe komai ta sanar masa dariya yayi yana fad'in "Kinyimin dai² amma abunda ke so dake duk abunda za tayi miki ki daina biye mata kinji ko" "To BB in sha Allah hakan bazai sake faruwaba" "Yawwa CWEETY" Motan shiru suka d'auki hanya....... 《《》》 "Aikin banza aikin wofi tarho d'inma tsabar tsiya irin ta y'an garin nan an rasa wanda zai taimaka ya kiramin MA'U naji halin da ake ciki.. Gashi ta barni da bashi fal kaina,gashi har yau ta gagara zuwa garin nan,kuma babu wani aike da tayimin,ba danma boka na saman dutse yana taimakona ba da yanzun mutanen dake bina bashi duk an mantar da su ba da sun zo sunmin rashin mutunci" Ita kad'ai sai surutai take kamar wacce k'wak'walwarta ta kwance "Amma babu komai,ai duk inda take dole wata rana zata kawo kanta zata ci gidansu a hannuna,ita da cin moriya wato ni kuma da wahala" Sai k'wafa take saki ita kad'ai talauci duk ya isheta,MALAM en kuma da take ta faman bankawa asiri babu wata mafuta da ta samu daga gurinsa,abunda take so babu dan kuwa bai samu ba dan kuwa so take ta dinga juyashi amma yak'i juyuwa,nasara d'aya da tayi kansa an rabashi da y'arsa abar k'aunarsa,ya manta da ita wanda yanzun ko maganarta bayayi.... Wannan kenan....... 《《》》 A gidan su KHALEEL kuwa tun da KHALEED yace masa ga shinan ya fito,daga yanzun zai taho yake ta faman jiran ganin zuwansa amma shiru,hakan ne yasa shi kiran line ensa... "MAN ina ka tsaya ne kam,kasa sai jiranka nake tun d'azun kace kana hanya fa" "Idan ka gama min fad'an sai ka ajiye waya muna bakin gate fito mu wuce" Daga haka ya ajiye wayan ba tare da ya kashe ba,saima hand's free da yasa ta... "Amma kai kam koi bak'in mugu maimakon ka kashe shi ne zaka sani a hand's free?" Dariya yayi mai sauti,KHALEEL na jin haka yayi saurin kashewa dan ya san KHALEED ba kashewa zaiba... Yana fitowa ya tarar dasu cikin motor en... "Aaaaaa!kace tare kuke da Momcynah" Sukayi murmushi dukkansu kafin suka shiga gaisawa.. "Ammm!nace ba" KHALEED ya kalleshi yayin da ita kuma ZUHRA ta sunkuyar da kanta k'asa tana murza hannunta... "Mu shiga ku gaisa da UMMI sai mu bar ZUHRA a nan muje mu dawo" "Noo! kada ka damu tare zamu je da ita,idan mun dawo sai mu shiga,ai ina jin nan zamu yini yau" "Wow! kace UMMI tana da manyan bak'i" "Ka jika da wata magana mune bak'in?" "Noo! sub'ucewa bakina yayi ya fad'i haka" sukayi dariya gaba d'aya su uku... Seat en baya ZUHRA ta koma daga nan motansu ta cilla kan titi sai police station.......... *_~TEAM KHUBRA.~_* *_REAL SMASHER._* 💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *22/ʝųŋɛ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* 🍰🍩🍯 🎂🎂🎂🎂🎂 🌹🌹🌹🌹 *~HAPPY HAPPY BIRTHDAY.. ~* _May it be the best day of your life thus far, & may your happiness grow with each passing day through the many many birthdays that surely are ahead of you._ *~HAPPY BIRTHDAY TO YOU MY SISTER'S~* _NI'IMATULLAH M.U (AUNTY G) & RAHMATULLAH M.U (AUNTY U) wishing u many more blessing year's........Happy fruitful year's dearies._ 🎂🎂🎂 🎁🎁 _Here is my gift.._ 😋📦 *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *3⃣1⃣* *A* office en D.P.O aka sauke su,da yake ya d'an shiga ciki yana zagayen duba masu laifi.. Suna nan zaune kusan 30 minutes sannan ya shigo,ganinsu da yayi yasa shi sakin fuskarsa,yana mai mik'a musu hannu,sunkuyar da kawuna sukayi k'asa alaman girmamawa kafin suka bashi hannu.. Bayan sun gama gaishe² ya kallesu su duka coz bai san abunda ke tafe da suba a wannan safiyar "Ammm!me ke tafe daku?duk da dai nasan zuwan naku ba zai wuce kan yarinyar da kuka bada report na b'atanta ba" "Yallab'ai ba b'ata tayiba saceta akayi" ZUHRA tayi katsalandan d'in yin magana 'Dan murmushi yayi,kafin yayi magana BB ya rigashi duk da yayi maganar ne k'asa² ta yadda ita kad'ai taji me yace "Tambayanki akayi da zaki yi magana?" Bata kalleshiba ta d'an sunkuyar da kanta k'asa "Ehhh!tabbas kina da gaskiya ba b'ata tayiba saceta akayi,shin kina da masaniyar yadda al'amarin ya faru ne,kuma mene ne alak'arki da ita wacce aka sace en?" Sai da ta kalli BB tukun,ganin ya d'aga mata kai alaman tayi magana yasa tace "Ehh!yallab'ai tabbas ni witness ce akan wannan case en,kuma ni Y'ar uwace ga wacce aka sace ta jini" Kaf abunda ta sani na yadda al'amarin ya faru ta sanar da shi,sai dai abunda ta rage cikin labarin bata sanar da shi mahaifiyarsu ce tasa aka aiwatar da abunba,tana gama jawabi tayi shiru ba tare da ta sake cewa komai ba.. Dogon ajiyar zuciya ya sauke kafin ya fara magana "Shin ko akwai wani abu da zaki iya ganewa game da mutanen da suka aikata wannan d'anyen aiki? misali:kamannin wani ciki,suturan da suka sa da kuma mota ko number motan? Shin zaki iya gane wannan ko makamancin haka?tunda kinyi bayanin kuna tare lokacin da al'amarin ya faru" Kanta ta d'an d'age alamar tunani Fitowarsu daga gida zuwa aiken MAMA da yadda akayi al'amarin ya faru take tunawa,da sauri kuma ta d'ago "Yallab'ai bazan iya gane kamanninsu da number mota ba,amma motansu k'irar CRV ne bak'i sannan kuma kayan jikinsu duk bak'ak'e ne,sun rufe fuskokinsu da bak'in handkey idanunsu saye cikin black glasses,wannan shi ne kad'ai abunda zan iya tunawa game da su"... Shiru cikin office en yayi na d'an wani lokaci,baka jin komai sai kukan AC dake aiki... "Ammmm!gaskiya wannan case en yana da matuk'ar d'aure kai,da kamar ace mun samu photon ita yarinyar da aka sace sannan kuma an gane fuskar ko da mutum d'aya ne cikin masu laifin da sauk'i,ina tunanin aikin da sai yafi zuwa mana da sauk'i,amma duk da haka abun bai b'aciba... Yanzun akwai wani taimako da kuke buk'ata?" Yayi tambayar yana kallonsu duka... A hankali KHALEED ya d'an tab'a KHALEEL "Uhmmm!kai baza ka iya magana bane?" KHALEEL ya tambaya yana murmushin mugunta... Harara BB ya sakar masa sannan yayi gyaran murya,hankalin D.P.O na kansa jin yayi gyaran murya yasan akwai magana a gurinsa "Ehhheemm!yi maganarka muna sauraronka" "Yallab'ai dama kan maganar photo ne idan muka samo zaku iya nemota kenan?" "In sha Allah muna fatan samota duk inda take,saboda zamu baza photonta ne cikin garin nan,idan ma bata cikin garin nan zamu bada cigiya a kafafen sadarwa da yardar Allah zamu sameta" "To Allah ya taimaka yallab'ai,amma akwai wata alfarma da nake nema idan babu damuwa" "Fad'i maganar da kake son yi ina saurarenka" "Dama Yallab'ai ina son ka taimaka mana da y'an sanda da za suyi mana bincike ne su kuma lura da al'amuran wasu mutane,saboda akwai zargi akan su ina tunanin da hannunsu cikin wannan d'anyen aikin" "To! babu damuwa in sha Allah duka ai ba zai gagara ba,za ka bada address na inda suke idan yaso komai ake ciki zasu dinga sanar da kai" Basu suka bar police station enba sai da suka tabbatar sun samu mafita akan yadda zasu b'illowa al'amarin.... Suka yi masa sallama... Ta hanyan kasuwa yabi dasu,da mamaki KHALEEL yake binsa da kallo,sai dai bai kai ga tambayarsa ba yaga ya fice... Cikin kasuwan ya shiga da tambaya ya samu store en,tun da akayi maganan photo zuciyarsa ke ayyana masa abubuwa da dama,shi ya sama yanzun ba tare da yayi shawara da kowa ba ya shiga siyan kayan zane abun mamaki kamar wani Artist haka ya siya kayan,yaran store en suka bishi da kaya fal hannunsu... Cikin ZUHRA ko KHALEEL babu wanda yasan me yake shiryawa kamar yadda babu wanda yaga kayan da ya siyo aka zuba masa su a booth... Ya sallamesu suka kama hanyan komawa store,shi kuma ya shiga motor en yayi mata key zuwa gidan su KHALEEL... 《《》》 Tun safe kowa cikin su biyu BABA ZUWAIRA da kuma KHUBRA suka kama hanyar sana'arsu... 'Bangaren KHUBRA babu wani damuwa da yake a ranta wanda har zai dinga damunta a wannan lokaci,burinta bai wuce ganin ta kafa kanta a rayuwa ba,shi yasa ta jajirce dan ganin rayuwarta ta inganta.. Can k'asan ramin ta gangara,gurin babu mutane sosai sai y'an tsirari da suke d'iban ruwa suma,har ta gama tana shirin barin gurin wata matashiya ta matso kusa da ita fuskanrta a sake,da sallama a bakinta dai² lokacin KHUBRA tana niyyar haurawa sama "Sannu baiwar Allah" "Yawwa sannu" KHUBRA tana kallonta da mamaki ganin babu wanda ta sani a garin.. "Suna na HAFSAT ina zaune cikin garin ZAKIRAI,babana shi ne SARKIN KASUWA" "Allah sarki na gode" KHUBRA ta fad'a tana d'an murmushi.. "Kefa baki fad'amin naki sunan ba" "Suna na KHUBRA" "Amma ke bak'uwa ce a garin nan ko?naga ban san fuskarki ba" "Ehhh!haka ne,ban jima da zuwa garin nanba" "Allah sarki na gode sosai,sai mun sake had'uwa" Kowacce ta kama hanyanta,da yake ita KHUBRA ta riga ta gama abunda ya kawota gurin,ita kuma HAFSAT zuwanta kenan shi yasa tafiyan nasu ya bambanta...... 《《》》 "Oyoyo TAKWARA yau kam ina da manyan bak'i,yaushe rabona da ganin k'afarki a gidan nan,gaishe nima da kuke zuwa kun daina yanzu, ince ko HAJIYA MURJA ta hanaku zuwa??" "Wallahi UMMI abunda na fad'a kenan lokacin da KHALEED ya sanarmin wai nan zasu yini" Harara BB ya sakar masa ba tare da yayi magana ba... "Ai kuwa dai gaskiya KHALEED ya fad'a,kai dan gidanku idan kaje a matsayin wa kake zuwa??" "Aaaaa!UMMI nifa na fishi zuwa kinga kuwa dole na zama d'an gida,shi kuma idan ya zo nan bak'o ne" "A'a ni d'ana ba bak'o bane a gurina,kai ne dai ka maida minshi bak'o" "Yawwa UMMI gara da kika fad'a masa dama na fad'a masa ni ba bak'o bane a gurinki" "K'warai kuwa ka wuce matsayin bak'o a gurina,bama kaiba ko da wani ka kawo gidan nan wanda ban saniba ai bazan kira shi da bak'o ba,saboda matsayinsa ya wuce haka" "Lallai yau zuwanka yasa UMMI ta mai dani gefe kun had'emin head kai da UMMI,sauk'i d'aya Allah yaso nima ga k'anwata da yau ina jin sai nayi kuka" Yanda yake maganar ya bawa kowa dariya cikin parlor.... Yini guda sun k'auracewa gidan MAMA,sai dare suka yi niyyan komawa gida,turaruka masu kyau da tsada UMMI ta bama ZUHRA,suka rako su har bakin mota,sai da suka ga fitarsu daga gidan sannan suka juya.... 《《》》 Tun bayan fitarsu ZUHRA daga gida MAMA ta rasa abunyi,kallon y'ar lelenta tayi fuskarta duk ta soma tasawa saboda dukan da ZUHRA tayi mata... "Kin ga irin abunda nake fad'a miki ai,duk lokacin da kika takali yarinyar nan da fad'a sai nayi miki magana,daga yau ai ba sai na sake ce miki komaiba,gobema kya k'ara" "To ni MAMA me nace mata bayan itace bata da gaskiya dan kawai nayi magana shi ne ta zage nifa" "Ni dai ai bance miki komaiba,amma dai kam wata rana zaki ci ubanki a hannun YAYANKU,kinsan ba a tab'a ZUHRA a gabansa" Tura baki gaba ASHNA ta shiga yi dama gashi ya kumbure,abun dai sai wanda ya gani.... Yinin ranan MAMA tana zuba idon ganin ta inda su ZUHRA zasu shigo gidan amma shiru kake ji wai "MALAM YA CI SHIRWA"..... *8:40* MAMA ce cikin parlor sai kaiwa da kawowa take,abun duniya duk yayi mata yawa,ita kad'ai sai surutai take,ga wayan a hannunta amma ta kasa kiran KHALEED bare ta tambaye shi ina suka tafi,ganin ta rasa mafita yasa ta nemi guri tana shirin zama,horn data jiyo shi ya bata daman sake mik'ewa ta nufi hanyan fita daga parlorn.... A haraban gidan suka had'u lokacin yana k'ok'arin fitowa daga mota... "Kai daga ina kuke tun safe da kuka fita sai yanzu" Babu wanda yayi magana cikin su biyu,suka kama hanyan parlor,binsu ta shiga yi har cikin parlorn yanayin fuskar BB ya hanata sake yin magana dan ko yanda ya had'e fuskansa za kayi tunanin bai tab'a sanin wani abu da ya danganci dariya ba,wannan yanayin da ta gani shi yasa ta kasa sake yin magana.... Ita ko ZUHRA suna shigowa ta kalli BB da ya zauna tana fad'in "YAYANAH sai da safe" Kansa ya kad'a mata ba tare da yayi magana ba... MAMA sai kallonsa take amma ta kasa magana kan dole ta jaa bakinta tayi shiru,dan tana da tabbacin ko tayi maganar ba kulata zaiyi ba,tunda y'an miskilancin suka motsa.... Zaman gurin ne ya isheta haka ta tashi ba tare da ta samu abunda take nema ba,tana barin gurin shima BB ya mik'e da niyyar barin gurin har ya d'auka hanyan bed room ensa,ko me ya tuna kuma ya dawo,fita yayi har parking lot,booth ya bud'e duk kayan dake ciki ya fito da,d'iban kayan yayi a hankali ya shiga dasu bed room en... Fito dasu ya shiga yi d'aya bayan d'aya ya baje komai,k'aton allon ya kafe a tsakiyan bedroom en nasa yanda ko da mutum ya tashi daga bacci da shi zai fara arba... Toilet ya shiga ya sakarma kansa ruwa,ya jima k'asan shower kafin ya fito,ba tare da ya b'atawa kansa lokaci ba ya zira farin singlet da boxers,sai sprays da perfume's da ya bajewa jikinsa kamar ba gobe... Bacci ya k'auracewa idanunsa ,dai² lokacin wall clock en d'akin ya nuna 10:30pm.... Idanunsa ya rufe yana tuna wasu moments nata,a hankali ya bud'e idanunsa masu haske ya sauke su kan allon da ya shimfid'a white card board paper... Sake rufe idanunsa yayi bayan ya d'auki alk'alamin,cikin nutsuwa ya dad'a bud'e su,a hankali ya shiga zane saman paper en,abun gwanin sha'awa haka yake sarrafa hannunsa da yake d'auke da alk'alamin... Bayan shud'ewar wani lokaci ya dakata yana k'arewa zanen dake kan board en kallo,dai² lokacin idanunsa sun gama k'ank'ancewa kallon zanen dake jikin paper yayi,ya saki wani k'ayataccen murmushi,shi kad'ai yake surutansa,bed ya nufa bayan ya gama sumbatan picture en ya kwanta,dai² lokacin 12:00am... Bacci mai nauyi ya d'auke shi cike da mafarkin KHUBRA...... Da safe misalin k'arfe 11:00am ya fito cikin shiri hannunsa rik'e da paper ya fito sai k'amshi yake bazawa,har ya fita babu da wanda ya had'u haka ya fice daga gidan... Direct police station ya wuce,sergent da suke kan counter suna ganinsa suka shiga gaidashi saboda sun ganeshi office en D.P.O suka raka shi,dan sun san basa rakiyar banza... After sun gaisa da D.P.O ya shaida masa abun da ya kawo shi,take kuwa ya buk'a ci ganin pic en yarinyar da ya fad'a masa ya zo da shi,babu b'ata lokaci ya mik'a masa... Duk abunda ya kamata shi D.P.O suka tattauna akan yadda za a yad'a photon cikin garin Kanon dabo... BB ya masa godiya ya fito dan tafiya gida,wanda k'arshe ba shi ya bar station enba sai da D.P.O ya had'a shi da y'an sandan da zasu yi masa aiki suka gaisa,sannan ya wuce..... 《《》》 Kwanaki sun ci gaba da gangarawa b'angaren KHUBRA rayuwarta cikin nutsuwa babu wani abu dake damunta rayuwarta take babu takurawa... Kulawan da BABA ZUWAIRA ke bata ko lokacin da take gida hannun iyayenta bata samu irinta ba,shi yasa ta saki jikinta sosai babu damuwan komai cikin ranta.... Duk lokacin da BABA ZUWAIRA ta kalli KHUBRA tana tausaya mata irin rayuwar da take ciki,duk da ta kafu akan sana'arta ta *GARUWA* wanda yanzun ta kai duk line da zata gifta cikin garin na ZAKIRAI an santa,duk inda ta gifta za kaji ana fad'in *KHUBRA Y'AR GARUWA*,wannan d'aukaka da ta samu kan sana'arta yana mata dad'i da yadda mutane ke yabon halayenta cikin garin.... Wannan kenan...... *~KEEP FOLLOWING........~* *~TEAM KHUBRA.~* *_REAL SMASHER._* 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *23/ʝųŋɛ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* _AS'ALULLAHAL AZIIYM RABBAL ARSHIL AZIIYM AN-YASHFIYAKI *7_ _GWS duarling sis @CWEET HUBBEEY._ *~________________________~* _*AUNTY G & AUNTY U* suna matuk'ar godiya da sadaukarwarki garesu gurin taya su murnan zagayowar ranar haihuwansu,fatan Allah ya k'ara zumunci da k'aunar juna.....Ameen..._ _@CWEET HULBATEEY._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *3⃣2⃣* 🇹un bayan zuwansa police station lokacin da ya kai photon da aka buk'ata,yake jiran jin sakamakon binciken daga wajen D.P.O amma shiru,har ta kai ga yau tsahon kwanaki bak'wai amma shiru kake ji.... _WAI MALAM YA CI SHIRWA...._ B'angaren Police kuwa da aka had'a BB dasu tuni suka fara aikinsu ba tare da sanin HAJIYA MURJA ko HAJIYA LAURA ba,dan ko kowacce akwai masu kula da al'amuranta duk zirga² da suke a idon hukuma suke aiwatar da hakan... Shirun da BB yaji kwana biyu babu labari ne yasa shi kiran D.P.O yana neman k'arin bayani game da case en b'atan KHUBRA.... Cikin yanayin sarewa ya shiga kiran line en D.P.O,wanda cikin nasara ya d'auka ba tare da b'ata lokaci ba... "Hello!yallab'ai barka da rana,ya aiki?" Daga gefen D.P.O aka amsa masa "Lafiya,Alhamdulillah!" "Yallab'ai dama kira nayi na maka tuni naji kwana biyu shiru babu wani k'arin haske kan b'atan yarinyar nan" Daga gefen D.P.O aka amsa da "Ehhh!toh gaskiya nima dai abunda ya jima yana bani mamaki game da wannan case en shi ne,tun bayan da ka kawo photo da muka buk'ata aka watsa shi a kafafen sadarwa amma shiru har yanzun babu wani bayani da muka samu daga gurin al'umma,munyi nema munyi cigiya amma shiru har yanzun babu wani ci gaba,ina ganin dai kam sai mun k'ara hak'uri,mun kuma k'arawa abun lokaci muga yadda Allah zai yi ikonsa.. Amma har yanzun muna kan bincike da izinin Allah zamu sameta"..... Dogon ajiyar zuciya BB ya sauke kafin cikin kasala ya furta "Allah ya bayyana ta" D.P.O ya amsa da "Ameen" Sannan ya d'ora da fad'in "Ina fatan dai yaran da muka turo suna kan aiki,babu wata matsala da ake fuskanta" "Ehhh!Yallab'ai babu wata matsala,aikinsu yana tafiya yadda ya kamata babu wata matsala" "Ok! Babu matsala Allah ya bayyanata,amma a k'ara hak'uri" "In sha Allah yallab'ai,na gode sosai" Sukayi sallama,bayan BB ya ajiye phone en ya jima yana nazari kan wannan case en,shi kad'ai kuma ya mik'e ya zari car keys ensa ya fice... 《《》》 Tsaye take cikin super market en *JIFATU STORE* dai² b'arin y'an rugs tana dubawa... Wayanta ne yayi k'ara a hankali ta bud'e jakarta ta fito da ita.. Rashin gaskiya ne yasa ta juyawa tana kallon yanayin gurin,babu kowa a arean da take shi yasa ta d'auki kiran ganin sunan dake lilo kan wayan... "Hello HAJIYA MURJA kiyi hak'uri bana gida ne,shi yasa ban d'auki kirankiba,amma ki bari na k'arasa gida,yanzun ina *JIFATU* naje siyayya" Daga gefen da aka kira cikin fad'a² ake magana wanda har wayan me magana ta farko tana amsawa k'asa²,ta yadda idan akwai wani a kusa zai iya jiyo abunda ake fad'a... "Haba HAJIYA LAURA tun yaushe nake kiranki kink'i amsawa,idan abun nan ba mai yiwuwa bane yaci ace kin sanar dani,amma kin barni kara zube... Waima dan Allah wasu sha³n kika sa suka yi aikin nan?" "Haba HAJIYA MURJA nafa fad'a miki bana gida,kiyi hak'uri zan kiraki idan naje gida" "Kinga HAJIYA LAURA dakata bana son jin wannan maganar daga bakinki kawai idan zaki tsaya muyi magana to idan kuma ba hakaba,wallahi zan zare hannuna a ciki duk lokacin da wannan lamarin ya kwab'e kada kiyi kuka da ni,kiyi kuka da kanki... Kina da damar aikata duk abunda kika so,zab'i ya rage ga mai shiga rijiya.... Ko ki bani had'in kai muyi magana yanzun ko kuma ki kashe,duk lokacin da kikaga dama kya neme ni".... Tana kaiwa nan tayi shiru tana sauraren jin me HAJIYA LAURA zata ce... A gefen HAJIYA LAURA kuwa jin furucin na k'awar tata ya so ya bata tsoro amma ta dake tare da cizon leb'enta na k'asa,sai da tayi gefe da wayan sannan ta saki k'wafa.... "Babu damuwa muyi maganar yanzun" Murmushin mugunta HAJIYA MURJA tayi sannan ta fara magana "Ai ke nake sauraro naji baki cemin komai game da tambayan da nayi miki ba " "Wane tambaya kenan?" "Ce miki nayi wane sha³i ne suka yi wannan aikin?ina nufin wane gidadawa kika sa suka zo gidana ranan da aka sace yarinyar nan?" Maganar HAJIYA MURJA ba k'aramin b'atawa HAJIYA LAURA rai tayi ba,haka ta danne tana bata amsa.. "Wasu yara ne da sukemin aiki,wani abu ya faru ne?" "A'a kawai dai ina son sanar dake ne duk inda suke idan har suna cikin garin KANO to suyi gaggawar barinsa domin kuwa yaron nan ya tsananta bincike... Sannan abu na gaba idan har sukayi abunda ya janyo aka kamasu to ki tabbatar musu da kada su sake suna na ya fito a cikin bakunansu... Kuskuren dake cikin ambaton suna na dai² yake da rasa rai,na fad'a miki saboda haka ya rage naki,ko ki jaa musu kunne ko ki k'yalesu su aikata hakan" Cikin sanyin jiki HAJIYA LAURA ta amsa,amma cikin zuciyarta cike take da tarin k'unci... "Sannan abu na gaba ina so ki kula da duk wani al'amura naki,idanuna suna kanki,kuskure d'aya kikayi zaki ki hannun hukuma".... Ita dai HAJIYA LAURA bata iya cewa komaiba,baya ga zuciyanta dake tafasa,wanda idan ka kalleta zaka iya gane tsananin b'acin rai da take ciki a kan fuskanya..... Bayan sunyi sallama ne HAJIYA LAURA ta fara magana cikin b'acin rai ta furta "Lallai HAJIYA MURJA wato ni take son mai dawa bagidajiya,to wallahi sai na koya miki hankali,zaki san dani kike zanc en".... Cikin b'acin rai ta fice daga gurin ba tare da ta siya abunda ya kawota ba,ta kama hanyan komawa gida.... Zuciyarta tayi k'unci da maganganun da AMINIYAR tata ta gama yab'a mata,ita kad'ai take k'wafa idan ta tuna abun duniya duk ya isheta...... 《《》》 "Hello!sir" Aka ambata daga b'angaren mai kiran,wanda yake magana k'asa²,da alama kuma akwai wani babban al'amari a tare da shi da yake son sanarwa... Bayan an amsa masa ya shiga koro jawabi... "Yallab'ai akwai wata mata daga cikin assignment da aka bamu, yau nabi bayan matar zuwa *JIFATU STORE* dake kan hanyar *OBASANJO ROAD*... Tabbas yallab'ai akwai wani al'amari a tare da matar,kuma daga dukkan alamu matar bata da gaskiya duba da yanayin yadda take magana a waya,da kuma yanayin data fito daga *STORE* en..." "Cikin wane irin yanayi kaga ta fito?" "Yallab'ai yanayin da ta fito yana nuna tana cikin tashin hankali" "Shin akwai wani abu da ya faru? ina nufin wani abu ya faru da ita bayan shigarta gurin siyayyar?" "Ehhh!yallab'ai bayan shigarta da kamar minti uku (3) naga ta d'auko waya a cikin jakarta ta hannu,to yallab'ai bayan ta amsa kiran wayan ne naga hankalinta ya tashi ta fito"... "Lokacin da take wayan kana ina kai en?" "Yallab'ai ina cikin gurin da ta shiga" "Ok!ina fatan babu wanda ya kula da binta da kake" Cike da ladabi Sergeant en ya furta "A'a yallab'ai babu wanda ya gani" "Da kyau aikinka yana kyau,abunda nake so da kai kaci gaba da bibiyarta,har mu tabbatar da gaskiyan abunda muke hasashe. Allah ya taimaka"... Daga haka sukayi hanging wayan... Tunani BB ya tsaya bayan ya gama answering call en daga sergeant en,akan hanyarsa ta zuwa gidansu KHALEEL... Da kyar ya katse abunda yake yama motan key zuwa gida,dan ji yayi bazai iya zuwa ba,hakan ne yasa shi canja shawara ya koma inda ya fito.... 《《》》 Kwanaki sun ci gaba da giftawa kamar ana ingizasu.... Ta b'angaren binciken neman da akewa KHUBRA abu ya faskara dan ko zuwa wannan lokaci har an gama fidda rai,anyi cigiyan anyi neman amma shiru kake ji uwa an shuka dusa,wannan dalilin yasa BB yanke shawaran sawa a tsananta yin rok'on Allah game da matsalar duk da kuwa dama anayi amma yana da burin na wannan lokacin yafi na baya... Haka kuwa akayi ko da ya tuntub'i KHALEEL bai yi k'asa a guiwaba ya amsa masa da fad'in "Tabbas wannan ma shawara ce ya kamata muyi hakan,Allah dai ya bayyanata idan muna da rabon sake ganinta" Suka amsa da amin cike da jimami.... 《《》》 Zaune take cikin parlor ta hard'e k'afafunta d'aya akan d'aya,ta cije leb'e ta gama cika tamkar zata fashe... Iska ta furzar mai d'umi tare da fizgo wayarta tana latsawa cikin fusata take magana.. "Haba BIGGY sau nawa zan sanar maka da ina nemanka,ko kuwa so kake sai raina ya gama yin duhu kafin ka zo?" 'Dan dakatawa tayi tana sauraren me zai fad'a "To amma me yasa baka sanarmin da bakwa garin nanba ka b'oye??" "Tuba nake ranki ya dad'e amin aikin gafara" "Shi kenan amma magana nake son yi da kai mai matuk'ar muhimmanci,wanda bana son kowa ya sani,bayan ni da kai sai kuma yaranka,ka dai fuskanci me nake nufi ko?" "Ehhh!HAJIYA amma idan babu damuwa kiyi maganarki yanzun kawai saboda bana son zuwa gidanki saboda tsaro... Idan kuma wani aiki nema kiyi min bayanin yadda kike so ya kasance,za ayi miki duk abunda kike buk'ata"... Jin furucin BIGGY ne yasa ta sakin murmushin mugunta kafin ta fara magana "Toh! shi kenan,amma da san samu ne da ka zo gida ka same ni idan ya so sai muyi maganar,amma tunda ka sanarmin uzurinka na karb'a hakanma babu damuwa".... Sai da tayi shiru na wasu y'an lokuta sannan ta soma magana "Ka san me nake so da kai BIGGY?" Daga gefensa ya amsa mata da fad'in "A'a HAJJAJU" "Ina son duk inda kuke ku je gidan dana saku aiki kwanakin baya,akwai wata yarinya da nake son ku satomin,amma idan kun sace ta kuyi nesa da ita bana son kuma a samu matsala kan wannan aiki,ina son kafin ku satota kuyi bincike sannan kuma ku tabbatar da babu wanda ya ganku... Zan turo maka da photon yarinyar da zaku sato sannan ku tabbatar idan kun saceta kun sanar da ni a lokacin bayan kun d'aukota... Ina fatan ka fuskance ni ko?ni kuma zanyi maka bayanin abunda zakuyi bayan nan,da fatan baka manta kwatancen gidanba"... Dariya BIGGY yayi mai isarsa kafin yayi magana "Amma HAJIYA ba dai yarinyar da muka sace ce ta dawo ba ko?" "A'a wannan daban da waccan,wannan da nake son ku sato ina son 'DAUKAR FANSA ne akan mahaifiyarta,saboda ta nunamin ban iyaba shi yasa nake son ajiye mata DARASIN RAYUWA".... "An gama ranki ya dad'e kamar anyi an gama wannan aikin,za muyi duk yadda kikace" Sai da suka gama kitsa duk wata mugunta sannan sukayi sallama... Zuciyar HAJIYA LAURA fal da farin cikin wannan al'amari tana zaune tana kad'a k'afa sai sakin murmushin mugunta take....... _AYI DAI MU GANI...._ 《《》》 *3 MONTH LEAP.* KHUBRA ce rik'e da kuran ruwanta na sana'ar *GARUWA* k'afarta sanye cikin takalmin *FILLO SHOES* daga saman kanta ko ta kifa *HAT* na gargajiya,takalmin duk ya sha d'inki saboda gajiya da yayi.. Wani yaro ne ya gifo a guje daga wani k'aramin gida yana fad'in *"Y'AR GARUWA* ki kawo ruwa gidanmu za a siya" A hanhali taja hulan dake kanta baya kad'an tana kallonsa,fuskanta da d'an fara'a duk da yadda tayi duhu fatarta duk tayi wani iri abun tausayi... "To amma zo nan" Ta umarci yaron da yake shirin komawa a guje,jin ta kira shi ne ya matso.. Kunnensa ta d'an kama a hankali tana fad'in "Suna nane baka saniba ka kirani da *"Y'AR GARUWA"* ko kuwa iskanci ne yasa kayi hakan?" "A'a na sani" Ya fad'a yana dafe gefen fuskarsa ta side en da ta rik'e kunnensa.... "Daga yau naji ka sake fad'in wannan sunan sai na mareka,kaji ni ko?" Da sauri yaron ya gyad'a kansa alamar yaji kuma ya bi... "Yawwa k'anina,maza to ungo wannan" Ta sa hannunta cikin jakar dake d'aure jikin west enta ta fiddo da sweet.... Da murnansa ko ya karb'a yana tsalle,yana fad'in "Daga yau idan ban sake fad'a ba zaki dinga bani alawa?" "K'warai kuwa zan dunga baka" "YEEEE!ya" fad'a yana tsalle "Idan zaki dinga bani har YAYA zan dunga ce miki kinji ADDA KHUBRA" Murmushi KHUBRA tayi tana shafa kansa cikin so da kulawa.. "Maza to jeka gida gani nan zan kawo muku ruwan kaji?" A guje ya juya ya shige gidan cike da murna... Tana kallon shigewarsa ta d'an tsaya tana murmushi ita kad'ai tasan halin da ta shiga lokacin da taji yaron ya kirata da ADDANSA,wani siraran hawaye ne yayi layi akan fuskanta,da kyar ta tsaida hawayen nata tana mai goge su....... ~Ni da nake gefe cike da tausayin halin da take ciki "nace KHUBRA har yanzun kina nan da halinki na son kuka"...~ ~My HULBATEEY kuwa hawaye naga tana sharewa kan tsananin tausayin yadda taga KHUBRA ta koma....~ *_~KEEP FOLLOWING FAN'S....~_* *~TEAM KHUBRA.~* *_REAL SMASHER._* 💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *24/ʝųŋɛ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* _Wannan page tukuici ne gareku masoyana tabbas ina jin dad'in kasancewa tare daku kuma ina jin dad'in addu'o'inku gareni Allah ya bar k'auna,jinjina gareku *Fatima Ibrahim,Fatima Zois,Fateema 🌹, Fatima M.D* dama duk wani/wata masoyin/masoyiyar *SMASHER* wollah ina matuk'ar k'aunarku har cikin jini da b'argona nake jinku,Allah ya bar k'auna,ina godiya sosai da sosai,ina yinku irin *#TOTALLY* en nan...*SMASHER* tace ana *_~#ANA MUGU MUGUN TARE..*_~_ *~________________________~* _*AYSHA B 《AESHAB》* wollah muma muna yinki kuma muna sonki,ki jima kiyi k'arko cweety Allah ya bar k'auna *SHDG* na godiya sosai bisa karamconki garesu.._ *~________________________~* _Masoya muna buk'atar ku tayamu addu'ah DURLING SIS babu lafiya,fatan zaku dubi buk'atarmu...Allah ya tashi kafad'unki cweet HUBBEEY._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *3⃣3⃣* *D* a kyar ta iya saita nutsuwarta ta kama hanyan shiga gidan da yaron ya fito d'azun,hannunta d'auke da robber 25 litters... Da sallama ta shiga gidan,bayan sun gaisa da matar gidan ta shiga juye ruwan da ta kawo cikin mazubin da aka nuna mata,bata kai da gama abunda ya kaita ba,ta jiyo yaron nan yana fad'in "Inna kinga alawana da ADDA KHUBRA ta bani d'azu" Y'ar yank'wananniyar matar da aka kira da inna ta kalli yaron tana d'an murmushi "Aaaaaa!aikuwa angode,Allah ya saka da alkhairi..... Ina fatan dai kace ka gode ko?" "Laaaa!inna na manta ban fad'aba" Yaron ya fad'a yana rufe bakinsa da hannu.. Ran inna ne ya b'aci jin furucin yaron dake gabanta,cikin fushi² ta janyo rigarsa "Sau naw nake fad'a muku duk wanda zai muku kyauta ku dinga cewa an gode,ko ban fad'a muku ba?" "Dan Allah inna kiyi hak'uri wallahi mantawa nayi" Kamar zaiyi kuka yake maganar "Aii ba dainawa za kuyi ba,ina jin saina fara k'wacewa zaku shiga hankalinku,tunda bakwajin magana" "Wollahi inna bazan k'araba" "Maza wuce kace mata ka gode,kafin na sab'a maka" Da gudu yaron ya matso kusa da KHUBRA dake shirin fita yana fad'in "An gode ADDA KHUBRA" Batayi magana ba sai murmushi da tayi kad'ai ta d'aga masa hannu,daga haka tayi waje tana sha'awar halayyan matar na ganin yadda tayi tarbiyyan yaranta..... 《《》》 Tun daga wannan lokacin da BIGGY suka yi magana da HAJIYA LAURA suke observation a unguwan na RIJIYAR ZAKI dai² area'n gidan na HAJIYA MURJA... Sai dai da yake suna da wasu ayyukan na daban a kuma gurare da dama yasa har aka d'auki lokaci mai tsayi ba tare da sun gudanar da aikin da aka sasu ba.... Kamar wani mahaukacin gaske haka yake acting ta yadda kowa ya ganshi ba zai iya ganewa ba cewa mahaukaci ne na gaske ko kuwa na bogi ne?.... Haka yake zagaye line en tun asuba daya shigo cikin unguwan yanata buge² da son korar flies dake neman hawan masa fuska,a k'ok'arinsa na tabbatar da cewa shi mahaukaci ne,kayan jikinsa duk sun yage bayaga wata annakiyar daud'a da duk tabi jikin kayan ta lafe kai ka rantse dama a jikin kayan aka halicceta.... 《《》》 Tun bayan wattani uku da suka wuce ne kuma al'amura suka tsaya cak,zuwa wannan lokaci gaba d'aya binciken da ake dangane da b'atan KHUBRA abun ya faskara a kamo bakin zaren,wannan dalilin ne yasa aka fawalla komai duk wasu lamura an mik'asu ga Allah... Ta inda BB yaq sallami Sergeant da suke masa aiki ta inda suka koma ma'aikata suka ci gaba dqa aikinsu kamar yadda dama suke yi.... A dai² wannan lokacin ne kuma MAMA taso b'allowa BB ruwa akan lallai itafa tana son yayi aure duk dan ta mantar da shi maganar KHUBRA.... Jin maganar ta MAMA yasa shi neman mafita babu shiri dan kam tabbas tunda wannan al'amarin ya faru baya jin akwai wata y'a mace da ta isa ya kalleta bare har ya furta mata kalmar soyayya.... Cikin kwanaki k'alilan ya gama shirinsa cikin sirri babu wanda ya sanarwa zai yi tafiya... Washe gari da safe ya shigo cikin sauri,a parlor suka had'u da ZUHRA tana fitowa daga kitchen... "Yawwa CWEETY ansa wannan" Ya mik'a mata leda en dake hannunsa "Maza ki adana shi naki ne kinji ko?" "Toh BB nah na gode Allah ya k'ara arzik'i" 'Dan murmushi yayi daga nan ya bar gurin yayi hanyan bedroom,abunda yasan yana da muhimmanci na daga documents ensa da visa en da yayi na barin k'asan ya d'iba ya gama sasu a envelop yana gama had'a kayan ya maida car keys ensa cikin drawer daga haka ya fito yana kulle d'akin.... Bedroom enta ta shiga da yake sauri take ta shirya time en tafiyansu school ya k'arato ne yasa ko bud'e ledan bata tsaya yiba ta sa cikin closet enta ta rufe.... MAMA na zaune cikin parlor su ASHNA suka fito cikin shiri zasu tafi school,lokacin suna mata sallama,daga haka suka fice cikin sauri dan time en suna gaf da makara... Duk da ba flight en safe zaibi ba,yana son fita ya je gurin KHALEEL daga nan yake son wucewa,a tunanin BB yin hakan kad'ai shi ne mafita a tare da shi... Da sauri shima ya fita lokacin har sun kaiga mota da driver zai kaisu,sai dai me suna zuwa driver'n yake shaida musu motan yayi faci kuma yanzun masu faci basu fitoba... Yana gama maganan su ASHNA suka fice ita da ZUHRA,FATAHIYYA da KHALEEFA.... Ganin sauri suke ne yasa ZUHRA maida HANEEF ya sanar da MAMA abunda ke faruwa,komawa cikin gidan yayi da gudunsa ya fad'awa MAMA matsalan da aka samu,kamar yadda ZUHRA ta fad'a masa.. "Toh ai kuwa idan haka ne sai dai kuyi saurin tafiya ku samu NAPEP dan kada ku k'ara makara"... Tun bayan fitowansu daga cikin haraban gidan ASHNA ke ta faman doka tsaki saboda tsaiwan da take... Da gudun dai ya sake fitowa yana d'an haki ya mik'awa ZUHRA kud'in hannunsa.. "YAYA ZUHRA gashi inji MAMA ta ce mu nemi NAPEP wai ya kaimu kada mu k'ara makara" "Toh!" tace ta kama hannunsa sukayi gaba,inda ASHNA da sauran suka mara musu baya,sai tsaki take takaici duk ya isheta... 《《》》 HAJIYA LAURA zaune cikin parlor ta hakimce kamar kowane lokaci k'afarta d'aya a saman d'aya tana girgizasu da gani zuciyarta fara tas take jinta duba da yanayin da dake shimfid'e saman fuskanta... Wayanta dake ajiye gefe tayi k'ara,sai da ta lek'a fuskan wayar kafin ta d'auka da sauri ta kara a kunnenta tana magana lokacin ne kuma mood en fuskarta ya sauya kad'an "Haba BIGGY me yasa kayi disappointing ena? Kai da nake tsammanin zuwa wannan lokacin komai ya kammala game da aikin da nasa ku amma shiru mak'atau... Me kuke jira ne kam har yanzun baku aiwatar da aikinba?" Daga b'angaren BIGGY ya amsa "HAJIYA ki k'ara hak'uri muna kan aiki ne har yanzun,matsalan kuma da aka samu yaran ba wani fitowa suke ba to jinkirin da aka samu kenan.. Amma har yanzu yarana suna kan aiki,a kowane irin lokaci za a iya aiwatar da aikin" "To shi kenan ina jiran kiranka dai kada ka manta" "Sai kin jini HAJAJJU" Ajiye wayan yayi ya d'an waiwaya gefe kamar mai neman wani abu... 'Dayan wayan da ke ajiye yayi k'ara da sauri ya fizgota ya d'auka "Hello!kai yaa?" Daga gefen da aka kira aka ambaci "Ogaa!yaufa dawa tayi nama yaran nan gasu nan sun fito amma ba tare da driver ba" "Kace me!?" "Oga ba wasa da gaske su na gani yallab'ai" Da k'arfi BIGGY ya fara magana "Ok!maza kabi bayansu kaji wane hanya zasu bi,mu kuma gamu nan zuwa yanzun" Yana gama maganar ya kashe da gudu² ya fice daga gidan yana mai k'walawa ragowar yaransan kira.. A gurguje suka fito suna tambayansa "Ogaa!lafiya kuwa?" Key ya cillawa mai jan motan yana fad'in "Maza kuyi sauri muje kada damar yau ta wucemu,yaran aka gani sun fito.... Yi sauri ka tada mota mujeee" Cikin k'araji yake maganar wanda kafin su farga shi har ya isa bakin motar... Tsawa yake dad'a doka musu,a guje suka shiga rububin shiga shi kuma mai jan motan ya tada motan suka fice a 360,sai unguwan LION'S WELL....... 《《》》 BABA ZUWAIRA zaune tsakar gida tana harhad'a kayan da zata fita gurin sana'arta... Tsaf ta kammala shirinta,tana shirin fita daga gidan ta hau rafkawa KHUBRA kira da ta shige toilet har yanzun bata fitoba... "Wai kam KHUBRA me kike yi ne har yanzu kink'i fitowa ki tafi" "Gani nan fitowa BABA yanzu zan fito" "Kin dai san sai kin dangana da rafi amma kin kama kinyi zamanki a band'akin,ko so kike rana tayi miki kam ai ya kamata ki fito haka ki kama hanya"... Cikin sauri ta fito,ta ajiye bokitin hannunta a gefe tayi cikin d'aki... Kallonta BABA ZUWAIRA tayi tana girgiza kai "Allah ya kyauta.... To ni dai nayi gaba idan kin gama ga abincinki nan a rufe,sai kin dawo Allah ya kiyaye hanya ya kuma bada sa'a".... Tana daga d'aki ta amsa mata,ita kuma ta d'auki hijab enta ta fice daga gidan.... Cikin sauri itama KHUBRA ta gama shirinta ta fito daga gidan tare da kulle k'ofar da padlock k'arami... Duk inda ta bi a hanyan garin kaga tana gaisawa da mutane kamar dama a garin ta tashi,wattani kusan biyar da zuwanta kenan amma babu wanda bai san sunanta ba,manya da yara dake cikin garin badan komai tayi wannan suna ba ko sai kan sana'arta ta *GARUWA* da ta rik'e da gaske babu wasa..... 《《》》 Gudun da motar keyi ne yayi yawa duk da haka basu sauraraba sai over taking wasu motocin suke inda suka saka ganye gaba da bayan motan,jami'an tsaron dake kan titunan duk sunyi tunanin gawane suka d'auko a motan,wannan dalilin yasa basu tsayar dasu har suka kusa *KABUGA UNDER PASS*.... 《《》》 Tun bayan fitowansa daga gida da yake ya riga su ZUHRA fitowa shima a k'afa ya fito zuwa titi kuma da yake tafiyan na namiji ne duk da BB baya irin tafiyan nan da sauri² hakan bai hana masa isa main road en da wuriba... Napep ya samu tare da masa kwatancen inda ya nufa,cikin sauri suka bar unguwan.... Unguwan shiru babu hayaniya,a bakin get ya tsaya,ya shiga laluben phone cikin pocket ensa line en KHALEEL ya kira,wayan ya jima yana ring ba tare da anyi answering call enba.. Kusan kira biyar ba a d'aukaba,har yayi niyyan juyawa ya kuma fasa,ya sake gwada kiran line en... Cikin alamu na mai bacci KHALEEL ya d'auka phone en had'e da sakin hamma yana fad'in "MAN yane? bacci nake yi ban san kana kiraba" "Toh ai sai ka fito gani a bakin get" Mikewa yayi ya zauna a saman bed en yana murza eyes ensa tare da tambayansa "Kamar yaya kana bakin get gidan bak'onka ya zama yau da bazaka shigoba kayi parking a waje?" "Noo! ba da mota nazoba,kawai ka fito kaga MALAM ina jiranka" Yana gama magana ya katse ba tare da ya jira jin me KHALEEL zai fad'a ba.... KHALEEL dake shirin magana yaji BB ya katse line en,hakan ne yasa shi sakin tsaki,cikin takaicin rashin jiran jin me zai fad'a ya sauka a bed en tare da d'aukan jallabiyan dake saman bed side drower yayi waje,yana tafe yake saka rigan.... K'aramar k'ofan dake jikin babban get en gidan ya bud'e tare da lek'awa ya kalli gabas da yamma,ganin BB tsaye jikin wall en gidan ya fito gaba d'ayansa... Hannu ya mik'awa BB yana d'an murmushi,shi kuma BB ya gimtse fuska saboda ya tsani jira,hakan ne yasa KHALEEL jan hannunsa sukayi cikin gidan.... Cikin bedroom en KHALEEL suka shiga nan suka zauna kan sofa en dake cikin d'akin.... Dafe pore head ensa yayi wanda hakan ya janyo hankalin KHALEEL ya dafa shi yana fad'in "MAN lafiya kake kuwa?" Sai da yayi tsaki tukun sannan ya shiga labarta masa abunda yake faruwa,da kuma hukuncin da yake shirin yankewa... Shiru KHALEEL yayi yana nazarin me ya kamata ya fad'a wanda aminin nasa bazai ma hakan wata mummunar fussara ta daban ba........ 《《》》 Tafiya suke har suka fito babban titin unguwan,suna tsaye suna sauraren napep da zai kaisu school en amma duk wanda suka tsayar sai yace ba can zaiba,suna tsaye wani mai napep ya yanko dai² inda suke ya tsaya... "MALAM nan zaka kaimu MUSA ILIYASU COLLAGE" "To ku hau muje" Black jeap ce ta yanko a guje ta biyo one way dai² zasu shiga aka zuge murfin motan ta baya aka fizgeta,ba tare da motan ta tsayaba ta sake harbawa tayi gaba... Ihunta shi ya dakatar da sauran da suke shirin shiga cikin napep en... Mai napep da ganin haka ya fizgi machine ensa bai tsayaba shima gudun kada a kira shi shaida ya arce a 180.............. *~KEEP FOLLOWING...~* *~TEAM KHUBRA.~* *_REAL SMASHER._* 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *25/ʝųŋɛ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *3⃣4⃣* *F*ATAHIYYA da sauran yaran dake tsaye ne suka fasa ihuu dan sunfi kusa da ASHNA,ZUHRA dake kusa da napep tana shirin shiga taga ya fizgi machine ensa ya k'ara gaba,da sauri ta dawo da baya har tana shirin fad'uwa.... Juyawa tayi da niyyar yin magana ihunsu duk ya rud'ata ta kasa magana sai raba ido da ta shiga yi tana neman ASHNA dake tsaye baya.... Tunda motar ta cilla kan kwalta bata sauraraba danko ko lokacin da ZUHRA ta waiwayo bataga motarba sai k'ura da ta bari a gurin..... "Wayyo Allah sun sace YAYA ASHNA,shi kenan mun shiga uku" Abunda ke fitowa daga bakinsu kenan cikin k'araji da gunjin kuka... Jiki a sanyaye suka d'auki hanyan komawa gida dan sanar da MAMA halin da ake ciki..... Suna tafiya suna kuka,ita kam ZUHRA da take bayansu ta sakosu a gaba sam ta kasa kukanma,tana tafiya tana fad'in "Innalillahi wa-inna ilaihi raji'un,allahumma ajirna fii musibatin wa-aklifna khairan minha".... Abunda take ta maimaitawa kenan har suka shiga cikin gidan... MAMA na zaune cikin parlor sai ganinsu tayi sun shigo sai ihu suke suna kuka... Mik'ewa tayi cikin sauri bakinta har hard'ewa yake gurin tambayan ba'asin me yake faruwa... Ganin babu wanda yayi magana cikinsu,ta shiga binsu d'aya bayan d'aya da ido,cikin k'araji MAMA ke fad'in "Kaiiiiii!kuyimin shiru,ku sanar dani me yake faruwa" Shiru babu wanda yayi magana cikinsu hakan ne yasa ta fasa k'ara tana dad'a fad'in "Wayyoo!Allah kuyimin shiru nace..... Ina ASHNATA?" Ganin irin tashin hankalin da take ciki ne yasa ZUHRA matsawa jikin MAMA tana k'ok'arin rik'eta,cikin taushin murya ta fara magana a hankali kuma cikin nutsuwa "MAMA ki zauna dan Allah zan fad'a miki abunda ya faru" Figze hannunta MAMA tayi daga rik'on da ZUHRA tayi mata cikin surutun da bata sanma me take fad'aba ta shiga girgiza ZUHRA tana fad'in "Maza sanar dani me ya sameta?me ya samu ASHNATA?" "MAMA kiyi hak'uri ki zauna tukuna zan fad'a miki" Kallonsu kawai MAMA take yi dan kam cikin wannan halin da take ciki tafi buk'atar su sanar da ita halin da ake ciki.. Jikinta babu ko mayafi ta nufi hanyar fita daga parlor cikin sauri tana sambatun "Tunda bazaku fad'aba zanje na dubota da kaina"..... Da gudu ZUHRA ta mara mata baya inda sauranma suka rufa mata baya... Iya k'arfinta ta bud'e murya tana fad'in "BABA kayi sauri ka rufe k'ofa kada MAMA ta fita" Aiko cikin hanzari BABA dake zaune yana shirin kunna radio ya mik'e cikin sauri ya rufe k'ofan ko da ta k'araso gurin babu halin fita,juyawa tayi tana kallon ZUHRA da sauran YARANTA da suka iso suma a lokacin "Kunk'i fad'amin abunda ya sameta ko?sannan kuma kun hana ni na fita nemanta,me kuke nufi kam??" Duk maganar tana yine cikin hargowa.... "MAMA wasu sun sace YAYA ASHNA a mota" FATAHIYYA ce tayi maganar,take ko MAMA ta dafe kanta dake barazanar fashewa,fuskarta ta shiga yamutsawa,bakinta kuma yana motsawa a hankali,ba tare da sautin da take furtawa ya fitoba ta sulale k'asa........ 《《》》 "Kaga MAN bana son ka d'auki wannan matakin ina son kayi hak'uri ka koma gida,kayima MAMA bayanin da zata fahimta" KHALEEL yayi maganar cikin alamu na mai rarrashi,hannunsa d'aya yana kan sholder en BB... Ture hannunsa BB yayi daga jikinsa cikin fad'a² yake magana "Ehhhh!dama mana dole kace haka tunda ba kai ne a matsayin da nake cikiba shi yasa kake tunanin zan koma gida ko??" "A'a MAN sam maganata ba haka take ba,ina son dai ka tsaya ka fuskanci wani abu guda d'aya ne... Sufa iya wajibinmu ne yi musu biyayya nasan kasan da haka,sai dai shaid'an yana neman yin nasara akanka,wanda nake son kayi gaggawar dawowa hanya... Dan kam idan har ka bari shaid'an yayi nasaran sawa ka aikata abunda kake niyya to tabbas ka fad'a halaka... Dan Allah BRO kayi tunanin maganata kafin ka yanke hukuncin da kake tunanin d'auka".... Shiru KHALEEL yayi yana nazarin aminin nasa da yaga ya fad'a duniyar tunani,d'an tab'a shi yayi kad'an kafin yaci gaba da magana "Tunani mai zurfi ba shida wani amfani,kayi k'ok'ari ka saita kanka,kada kayi saken da shaid'an zaiyi tasiri akanka" "Haba MAN ta yaya MAMA zata wani d'aukomin maganar aure yanzun?bayan ni ban tab'a ce mata ina da wata yarinya da nake son auraba.. Duk wannan shirin na MAMA tana yi ne dan ta k'untatamin bayan RAYUWAR K'UNCI da ta dasa mana a baya wanda har yau babu wanda yasan takamaimai en gaskiyar al'amarin,amma a yau zan baka labarin GASKIYAR LAMARINMU ko dan ka fuskanci nufina...... Kamar mai nazarin wani abu ya d'an d'aga kansa sama kafin ya fara magana... *"ASALIN LABARINMU"* _"Shekaru ashirin da shida baya 26"_ "Iyayenmu sun kasance sunyi auren soyayya ne da juna kamar yadda labari da kuma yadda na taso na gani a shekarun baya kad'an,kamar yadda ka sani mahaifina sunansa *ALHAJI SAFWAN ABDALLAH* babban d'an kasuwa wanda aka sanshi kan kasuwancin man fetur a y'an shekaru da suka gabata wanda akewa lak'abi da *MAI DA AKWAI*... Asalin Mahaifina d'an jihar JIGAWA ne cikin DUTSE,a lokacin da mahaifiyata take bani labari race min,"sunyi aurene irin na soyayya,kuma ita ta kasance d'aya daga cikin y'ay'an abokin kakana wato mahaifin ABBANA kenan,bayan sunyi aure da shekaru 3 Allah ya azurta su da samun d'a namiji wanda ba kowane wannan yaronba sai ni,sun raineni cikin so da kulawa duk da a lokacin mahaifina baiyi suna ba kamar yadda kowa ya sanshi daga baya... Asalin sana'ar mahaifina ya gajeta ne tun iyaye da kakanni wato noma da kiwo,Allah ya sanyawa mahaifina nasibi ta yadda a gonar da kakana ya bashi yake noma bayan yayi aure,yana noma kayan amfani na masarufi,a duk lokacin da ABBANA yayi noma yana ajiye na amfanin gida sannan kuma yakan fitar da zakkah duk k'arshen shekara kamar yadda addini ya tanadar,ragowar kayan kuma yakan d'auka ya kaisu kasuwanni domin samun abunda zai b'atar.... Akan wannan d'abi'a tasa ne Allah ya had'ashi da aboki wanda ba kowa bane face ABBANKA,shi ya taimaki mahaifina har ya dawo cikin garin kanon dabo da zama ta hanyar bashi shawara akan ya dinga kai amfanin gonarsa da yake siyarwa kasuwannin garin kano saboda kasancewarta cibiyar kasuwanci... Bayan mahaifina ya amince da shawaran da ABBANKA ya bashi ne,yaje neman sulhu da kakana alokacin kaka yak'i amincewa a kokarinsa na cewa duk cikin y'ay'an da Allah ya bashi babu wanda ya tab'a yin nisa da shi,amma ganin yadda mahaifina yake rok'onsa ne yasa ya amince tare da yi masa fatan alkhairi.... A lokacin mahaifina kan zo ya koma a duk lokacin da ya gama kasuwancinsa,sai dai bayan wani lokaci yaga zirga-zirgan yayi masa yawa,to alokacin ne kuma ya nemi shawaran KAKA akan yana son neman gida saboda yadda al'amuran kasuwancin nasa suka dad'a bunk'asa,ba a b'ata lokaci ba KAKA ya amince masa saboda yadda yaga Allah yana bud'a masa duk a dalilin kasuwancin da ya fara"... "A gurguje nake son baka wannan *SARK'AK'IYAR LABARIN* fa..... Bayan haihuwata da sukayi wanda ni asali an haifeni ne a garin DUTSE,JIGAWA STATE saboda haka dani suka dawo garin kano,tun daga ni basu sake samun haihuwa ba sai da na kai kimanin shekaru takwas da haihuwa inda a lokacin har na fara zuwa makaranta,sannan aka haifi k'anwata ASHNA inda itama tana da shekara d'aya a duniya MAMA ta sake haihuwan ZUHRA,bayan wannan lokacin ne Allah ya kawowa ABBANA bud'i bayan bin shawaran da Abbanka yazo masa da shi kan su had'a jari su fara harkar man fetur,cikin ikon Allah da nasara kuma Allah yasa musu nasibi cikin abunda sukayi niyya.... Bud'i ya dad'a zuwa musu wanda a lokacin ne kuma aka kuma samun k'aruwa a gidanmu na haihuwan FATAHIYYA,bayanta sai KHALEEFA wato mai sunan KAKA kenan ABDALLAH,bayansa sai HANEEF wanda aka sama sunan mahaifin MAMA kenan,daga Kansa ne kuma haihuwa ta tsaya"... Kadafa kace ina yanke maka labarin ina yin hakane saboda nasan kasan hakan,sai dai ina son kaika k'arshen labari.... Tohh!a shekarun da suka gabata tun bayan haihuwan HANEEF ne kuma aka soma samun sab'ani tsakanin ABBA da MAMA tun lokacin da taji zancen yana k'ok'arin k'ara aurene ta tada hankalinta,idan baza ka mantaba a kwai wata k'awarta mai suna HAJIYA LAURA ko?" Kai KHALEEL ya d'aga masa,ci gaba BB yayi da magana "Wannan matar ita ce silar faruwar komai... A lokacin MAMA ta sameta da maganar ABBA yana son k'ara aure,bayan da can baiyiba sai yanzu da yaga yayi arzik'i duk dan son ya wulak'an tata... Nan ne itama HAJIYA LAURA ta shiga bata shawarwarin banza wanda MAMA ta biye mata sunata kitsa abunda za suyi,ana haka ne duk basu san da cewa ABBA ya dawo gidanba,kuma duk abunda suke tattaunawa yana saurarensu.... Jin maganar da suke hankalinsa yayi matuk'ar tashi wanda a k'arshe ya yanke shawaran samunta suyi magana ta fahimta.... Sai dai kash! a lokacin da ABBA ya samu MAMA kan maganar sai ta nuna masa itafa sam bata amince da maganar k'ara aureba,inda sukayi ta samun sab'ani wanda a k'arshe dai ABBA ganin ta dage yasa shi d'ebo duk wani kadara nasa ya zube mata ya kuma d'ora da fad'in "Ga abunda kikewa nan nasan dai duk auren da kike cewa bakya so nayi akan wannan abun kikewa ne ko?to gashi nan na baki,sai dai magana d'aya zan fad'a miki ki kulamin da yarana ki basu ilimi ta kowanne b'angare wannan kad'ai ya isheni,ni zan tafi bazaki sake ganinaba daga yau kin amince da wannan zab'in? Bud'ar bakin MAMA kuwa tace "ehh taji ya tafi duk inda zashi,tunda tana ganin ai ya bar mata komai na dukiyar da ya mallaka.... Tun daga wannan ranar bata sake ganin ABBA ba ya kama hany ya tafi.... Idan baka manta ba ai ka tuna lokacin da akace ABBA yayi accident ko?" Nanma kai KHALEEL ya sake d'agawa... "Abunda ya faru a wannan lokacin duk shiri ne wanda MAMA da babbar aminiyarta HAJIYA LAURA suka shirya duk dan kada duniya ta zagesu akan abunda ya faru shi yasa suka b'atar da hankulan jama'a amma ABBA yaba raye,k'asar ya bari gaba d'aya"... Shiru BB yayi yana dafe kansa,KHALEEL dake zaune ya hau fad'in "Toh!amma ta yaya kai kasan wannan labarin?" Sai da yayi wani murmushi mai ciwo tukun sannan yace "A lokacin da akace ABBA ya rasu idan zaka tuna ai ba a kawo gawaba ko? Toh bayan y'an zaman makoki sun watsene na samu MAMA kan maganar,akan lallai sai ta fad'amin abunda yake faruwa ita kuma tak'i bayan na takura matane kan zan sanar da hukuma idan har bata fad'aminba shi ne ta bani wannan labarin da kaji a yanzun".... "Innalillahi wa-inna ilaihi raji'un" KHALEEL yake ta maimaitawa had'e da dafe kansa,ya rasa me ke masa dad'i..... 《《》》 Mik'ewa ZUHRA tayi a fusace daga kan MAMA da ta fad'i tana fidda hannu ta wankewa FATAHIYYA fuska da mari "Ke wace irin sha³ ce da zaki fad'a mata wannan maganar bayan kina kallon yanayin da take ciki?" Bata iya maganaba saboda tsananin b'acin rai da kuma haushin FATAHIYYA da take jin kamar ta rufe ta da mugun duka a guje kuma ZUHRA ta juya ta yanki hanyan cikin parlor,a wayan MAMA ta lalubo number BB.. Kira ta shiga danna masa amma sam yak'i d'aukan ko guda d'aya,ga phones en a gabansa,sai dai baya jin zai iya d'aukan kiran nata... Ganin bashi da niyyan d'auka KHALEEL ya mik'a hannu tare da answering call en,yanayin muryanta ya tabbatar da ba lafiya k'alauba.... "Hello BB dan Allah ka dawo gida babu lafiya" Duk maganar da ZUHRA ke yi bata fuskanci ko dawa take maganaba,sai da taji yayi magana "Me ya faru?" "Wayyoo Allah!dan Allah MALAM ina mai wayar?shi nake nema please" Jin abunda ta fad'a yasa ya d'ago yana kallon BB tare da mik'a masa wayan.. Ko kallonsa BB baiba bare yasa ran zai amsa wayan,hakan da yayi ya tabbatar masa da ko kwana ne zasuyi a haka.. Hands free yasa wayan,cikin sheshshek'ar kuka ZUHRA ke fad'in... "Hello!Hello!! Dan Allah MALAM ka bawa mai wayar tun kafin mu rasata"... Fizge wayan yayi a hannun KHALEEL cikin wani irin voice yake tambayanta "CWEETY me ya faru kike kuka?" Duk yanayin yadda yajita ya gama d'aga masa tunani.. "Hello BB dan Allah ka dawo gida MAMA ce ta fad'i kuma bata motsi" "What!!!" ya fad'a yana mik'ewa... Ko gama sauraren abunda zata fad'a baiba yayi hanyan fita,da gudu-gudu,shima KHALEEL cikin sauri ya mara masa baya... Ko kafin ya fito har BB yayi waje,haka ne yasa shi saurin yiwa motan key ya fice daga gidan... Fitowansa ya tarar har yayi nisa cikin tafiyan da bai saba irinta ba,sai dai da gani kasan yana cikin damuwa... Tun kafin KHALEEL ya k'araso yake masa horn bai tsayaba,har ya k'araso kusa da shi,motan ya bud'e tare da masa magana "MAN ka dakata hakanan da wannan tafiyan kazo mu wuce" Juyawa yayi ya kalleshi cikin sakanni ya fad'a cikin motan,da mugun gudu suka bar unguwan sai gidan su BB..... 《《》》 Gudu suke shek'awa cikin mota, kamar wad'anda zasu tashi sama,duk da sun tserewa gurin da mutane zasu iya samunsu su cimmusu hakan baisa sun saurara ba... Fizge² take yi cikin motan duk kan ganin ta kub'uta,sai kai hannunta take tana k'ok'arin jan handle en dake jikin k'ofan... Mari BIGGY ya shek'a mata had'e da tsawa mai k'arfi wanda ta maidata cikin hayyacinta... Kanta ta kifa bisa cinyoyinta ta shiga rera kuka,su ko na cikin motan suna saurarenta amma babu wanda yayi yunk'urin dakatar da ita,ratse hanyan suka dinga yi wanda k'arshe dai sai gasu a *NA'IBAWA FLYOVER* nan suka ci gaba da fella gudu babu sassauci.... Straight suka yanki hanyan *BAUCI STATE* ba tare da sun sauraraba.. Tun ASHNA na kallon hanya har ta b'ingire take bacci yayi gaba da ita ba tare da ta shirya masaba... 《《》》 Ko gama tsaiwa motan baiba ya fito dan baya jin zai iya tsayawa har BABA MAI GADI ya bud'e musu get.. K'ofan ya tura ya shiga,a nan yayi arba dasu duk sun lullub'e MAMAN ko isashshiyar iska bata samu,ba tare da ya kulasuba ya shiga maidasu gefe,yana yin arba da MAMA bai jira jin komaiba kuma ba tare da yayi shawara da kowaba ya shiga k'ok'arin d'aukanta... KHALEEL da ya gama parking a gurin ya fito cikin sauri,kama masa MAMAN yayi suka sa a mota,ZUHRA tuni ta shige back seat kusa da kan MAMA suma suka shiga KHALEEL ya felli motan a 360.... *AKTH* suka wuce da ita direct babu jimawa aka shiga da ita EMERGENCY... Sama da 2 hour's likitoci na kanta babu wani ci gaba da aka samu... Zagaye gurin kad'ai BB yake hankalinsa duk ya gaza kwanciya,ZUHRA ko banda kuka babu abunda take,KHALEEL na kusa da ita sai hak'uri yake bata kan tayi shiru komai zai zama dai² amma abu ya faskara,saima k'aimi data k'arawa kukan nata... Fitowan babban likitan yasa su mik'ewa,wanda bai tsayaba saima cewa da yayi su biyo shi office.. Binsa kawai suke har suka isa office en sai da ya tabbatar sun zauna tukun ya shiga magana "Amm!kune wad'anda kuka kawo mara lafiyan ko?" KHALEEL yayi k'arfin halin cewa "Ehh!doctor" "Ok toh amma yaya alak'arku take da ita?" Nanma dai ya sake bashi amsa da "Y'ay'anta ne" Sai da DR en ya kallesu tukun,ya mik'a hannunta saman pore head yana share zufan da ya tsatstsafo masa da handkeey "Am so sorry... Gaskiya mara lafiyanku sai dai kuyi hak'uri............... *~Wayyooo shi kenan MAMA ta auza,ta wula.......~* 😨😨 *~#KEEP FOLLOWING........~* *_REAL SMASHER._* 💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *26/ʝųŋɛ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *3⃣5⃣* *"S* ai dai kuyi hak'uri amma gaskiya mara lafiyan naku tana cikin mawuyacin hali wanda tun shigarmu har kawo lokacin dana fito bamu samu ta farfad'o daga dogon suman da tayiba... Amma abunda ya d'auremun kai kuma abun damuwan shi ne akwai wani al'amari da ya faru wanda yayi matuk'ar tsoratar da ita da yayi sanadiyyar fad'awarta wannan hali,bayaga numfashinta da yake fita da sauri²... Cikinku akwai wanda ya sanar da ita wani abune?ko kuwa kun san abunda faru da ita?" A tare suka kad'a masa kai,alamar babu... To gaskiya sai kun kiyaye ba ko wane irin lokaci ake sanar da mutum wani abu da ya faruba,matuk'ar tsoro ya bayyana a tare da shi ko a tashe shi daga bacci dan sanar da shi hakanba,dan kuwa yin hakan ka iya jawowa mutum matsalar k'wak'walwa,wanda ba a fatan hakan ya faru... Sannan abu na gaba gaskiya muna buk'atar namiji babba,idan kuma kuna da wata da zata iya kula da ita to ya kamata ace kunzo da ita duba da har yanzun bata farfad'oba sai dai munyi nasaran saita numfashinta".... Shiru sukayi dukansu suna nazarin al'amarin,a hankali BB ya d'ago kansa idanunsa sun soma sauya colour zuwa red,a kan ZUHRA ya saukesu,sam ya kasa magana sai kallonta kad'ai da yake yi,zuwa wannan lokacin damuwarsa ta dad'a ninkuwa fiye da kowane lokaci da ya wuce.... KHALEEL ne yayi k'arfin hali bayan dogon ajiyan zuciya daya sauke,sannan ya bud'e baki da k'yar ya fara magana,dan kam suna buk'atar k'arin bayani kafin du samu mafita kan nemo wanda zai zauna da MAMA "ZUHRA me ya faru da MAMA ne kafin muzo gida?" Sai da ta saita kanta ta kuma goge fuskarta da tayi kacha-kacha da hawaye sannan ta kallesu su duka ukun DR,BB da kuma KHALEEL en,wani sabon hawaye ne ya sake tahowa,suna shirin zuba ita kuma sai kokawa take yi da su gurin ganin ta hana hakan afkuwa... "BB ASHNA" Abunda ta iya fad'a kenan hawayenta suka k'arasa zubowa... Wani uban tsaki BB yayi wanda yasa su kallonsa,tabbbas KHALEEL yasan mutumin nasa yana cikin matsananciyar damuwa... Hannunsa ya d'ora kan sholder ensa yana d'an shafashi kad'an alaman rarrashi "MAN take it easy,anything will be fine,ok?" Bai kula shiba kamar yadda ko kallonsa baiba,saima k'ure ZUHRA da yayi da kallo wanda har yafi na farko,burinsa bai wuce tayi magana ba,amma ita ta kasa gane hakan dan ya gama damuwa yaji,k'arshe kuma sai kawai ta wani ambaci sunan ASHNA kuma tayi shiru,to shi ina ruwansa da wata ASHNA?yarinyar da sam ba ganin girmansa take ba,shi duk zaman gurinma ya isheshi saboda takaici,a fusace ya mik'e tare da hararan ZUHRA dai² lokacin ta d'ago idanunta suka sauka kansa yana cillo mata wata uwar harara..... Shirin barin gurin da sukaga yana yine yasa su kallon-kallo,a hankali ta rik'o hannunsa tana kad'a masa kai.... Cike da fushi ya juyo "Da Allah ni sakeni kin sa sai jiranki muke muji abunda ya faru kin tsaya jama mutane rai,ko an fad'a miki MAMA jiranki za tayi ki gama kukan kafin ta tashi?? To idan baki saniba daga nan zuwa kowane irin lokaci zata iya mutuwa"... Da sauri ta d'ago ta kalleshi,dan tunda ya fara mata masifar ta sunkuyar da kanta,hawaye nabin fuskarta take fad'in "Dan Allah YAYA kayi hak'uri zan fad'a"... "Yi shiru ZUHRA ki sanar damu abunda ya faru kinga lokaci na dad'a k'urewa,kuma kinga DR mu yake jira yaji abunda yasa ta shiga wannan halin kafin musamo mafita.... Maza kinji fad'a mana me ya faru"..... Har lokacin BB na tsaye kamar wanda aka sama pause,ya kasa barin gurin kamar yadda ya kasa raba hannunsa dana ZUHRA... Shi kuma DR yana zaune sai kallon ikon Allah yake tsakanin wad'annan mutane.. Abunda ya faru ta kwashe ta sanar da su tun daga shirin tafiyansu school har zuwa lokacin da MAMA ta yanke jiki ta fad'i.... "Innalillahi wa-inna ilaihi raji'un" Shi ne abunda ke fitowa daga bakunansu,ba iya su kad'aiba hatta da DR en shima abunda yake maimaitawa kenan... Office en yayi tsiit babu wani sauti dake fita a cikinsa,sunyi shiru kowa da abunda yake tunani... KHALEEL ne ya katse shirun bayan ajiyan heart da ya sauke tare da fad'in "Dude gaskiya bai kamata muci gaba da zama a nanba,yanzun yaci ace mun sanar da hukuma b'atan yarinyar nan,tunda kaga wannan shi ne na biyu ya kamata ace mun dakatar da faruwar hakan"..... Ko kallo bai ishe shiba bare ya sa ran zai motsa daga inda yake,kallon mutanen gurin kad'ai yayi tare da ficewa cikin sauri kamar zai kifa... A baya ZUHRA ta shiga binsa da gudu-gudu saboda yayi mata nisa sosai lokacin da ta fito..... 《《》》 Daf da zasu shiga garin BAUCHI ya d'auki waya yana pressing,number HAJIYA LAURA ya laluba tare da kara wayan a kunne... Bata wani b'ata lokaci ba ta d'auka maganarta cikin isa da tak'ama "Hello!BIGGY ya akayi kuma?ina d'azun muka gama magana?" Yana dariya cikin wani irin voice had'e da shafa face en ASHNA dake tsakiyansu tana shek'a bacci yake fad'in "HAJAJJU!Allah ya taimakeki, yau dai munyi nasara kan wannan yarinyar,dan yanzunma haka mun d'auki hanyar BAUCHI saura kad'an mu k'arasa".. "Kaiii amma nayi farin cikin da na jima banyi irinsa ba... Ammmm!yanzun ina zaku sauka kenan?" Tayi tambayan tana jiran taji me zai ce da ita.. "HAJIYA ina ganin da mu kama hayan gida kawai kinga sai mu ajiyeta a nan har zuwa adadin kwanakin da za muyi" "A'a BIGGY kada ku fara,taya zaku samu gidan haya a hannun mutanen garin da basu sanku ba,bayan wannanma idan aka ganku da yarinya me kuke so ayi tunani,kana dai sane da cewa mutane zasu sanar da hukuma muddin aka ganku da yarinyar nan..... Abunda za kuyi kawai ku kama hotel a matsayinku na matafiya..... "Gaskiya HAJIYA bana jin hakanma mafita ce,dan kuwa duk wanda ya ganmu da yarinyar nan tabbas zai gane satota mukayi dan kuwa yarinyar kayan makaranta ne a jikinta... Ni ina ganin dai gaskiya ko dawowa za muyi KANO muna da gida kuma babu wanda zai san wani abu da yake faruwa"... "To kai da kasan da haka har ka bari kuka bar garin ko ma?" "HAJAJJU! wallahi na shiga wani shu'unin ne shi yasa na kasa tunawa,amma bari kawai mu dawo,tunda tahowarma ba wani amfani garetaba" "Ehhh!toh amma BIGGY kana ganin dawowarku a wannan lokacin babu wata matsala da za a samu?" "Babu hajiya,ina ganin tun kafin lokaci ya k'ure mana gara mu dawo kawai,ko ya kike gani?" Cike da jin dad'i HAJIYA LAURA ke magana,tana sakin wani uban smiling "A'a!tunda ka ce babu wata matsala dan kun dawoma babu wata damuwa kuyi hakan".... Juyawa BIGGY yayi ya kalli ASHNA da ta zame ta jingina a jikinsa tana bacci,sai da ya lashe lips ensa garin tunani har baima san lokacin da HAJIYA LAURA tayi magana ba... "Hello!hello!! BIGGY kana jina kuwa?" Yanayin yanda tayi maganar yasa shi dawowa daga duniyar da ya lula "Ehhh!HAJIYA ina saurarenki" "Yawwa to ina so ku kula da hanya,sannan kada ku kuskura kuyi saken da za a gane inda kuke... Ina fatan dai ka fahimci abunda nake nufi ko?" "Ehhh!HAJIYA za a kiyaye" "Toh shi kenan sai na jiku,Allah ya kiyaye hanya" Daga haka sukayi hanging kiran,kowa ya shiga duniyar tunani.... 《《》》 Yau tun safe da ta tashi take jin jikinta na mata ciwo,wanda ta rasa dalilin faruwar hakan.. A haka ta lallab'a ta shirya,ko abinci bata ciba take shirin fita... Kuran ta shiga kiciniya zata fita da ita BABA ZUWAIRA ta dakatar da ita "Haba KHUBRA yanzu haka kika zab'i zama?" Tsayawa tayi tare da juyowa tanama BABA ZUWAIRA kallon rashin fahimtar tambayanta,kafin ta bud'e baki tana shirin magana BABA ZUWAIRA ta rigata.. "Yanzu fisabilillahi ace ki tashi ba tare da kinci komaiba kuma ki hau shirin fita... To waima idan kin tafi baki ci komaiba zaki iya aiwatar da abunda kika fita dominsa?" Shiru tayi ta ci gaba da tsaiwa a gurin,sai dai wannan lokacin kanta na k'asa ta kasa magana... Jikinta ne ya sake yin sanyj jin furucin BABA ZUWAIRA,inda nan take ta tafi tunanin rayuwarta ta baya.. "Lokacin da take neman abinci ido rufe ta sanya a cikinta,a lokacin da take daf da mutuwa,amma ta rasa mai taimaka mata,yau gashi a rayuwarta taci karo da inda ake mata fad'a idan zata fita ba tare da taci abinciba"... Wasu siraran hawaye ta juya ta goge,sannan ta k'irk'iro murmushi lokackin da ta baro gurin da take "Eyyah!BABA yau tun da na tashi ne bana jin dad'i shi yasa banyi tunanin cin komaiba" Sai da BABA ZUWAIRA ta wurga mata harara kafin tayi magana "Dama haka za kice,abu da ko zuba abincin kikayi ba wani cin na kirki kike ba,kina cin abinci kamar ana bawa kyanwa" "Haba BABATA ina cifa da yawa" Harara ta dad'a wurga mata "Ke tafi can kya dai fad'awa wanda bai saniba,amma ba dai ni ba" Dariya sosai KHUBRA tasa,ta jima tana dariyan wanda har tasa BABA ZUWAIRA tsayawa da abunda take tana kallon ikon Allah...... 《《》》 "Dan Allah BB ka tsaya ka ji"... ZUHRA ce mai yin wannan maganar lokacin da ta kusa taradda shi,k'in tsayawa yayi ita kuma ta ci gaba da bagging ensa kuma ba tare da ta saurara da binsaba... Daga bayanta ta tsinkayo maganar KHALEEL "K'yale shi kawai ZUHRA kada Allah yasa ya tsaya" 'Dan juyawa tayi kamar za tayi kuka "Dan Allah YAH KHALEEL kace ya tsaya....please" "K'yaleshi dan kansa zai dawo kinji" Kanta ta d'aga alaman ta ji,sannan suka jera suna tafiya kowa da inda zuciyarsa ta karkata... Dai² d'akin da aka kwantar da MAMA suka k'araso anan suka tarar da BB zaune ya dafe kansa da hannayensa duka biyu yayi shiru... Tunaninsa bai wuce ta yaya zasu samo wanda zai kula da MAMA ba a zaman da za tayi a asibitin... Yayi zurfi cikin tunani KHALEEL ya zauna kusa da shi yana kallosa,phone ya d'auko cikin contact nasa ya shiga bincike,nan ya lalubo number D.P.O,har ya gama magana da shi BB bai saniba... Magana ya shiga yi masa amma sam bai san yana yiba har sai da ya girgiza shi,sannan ya kalle shi da rinannun idanuwansa da b'acin rai ya gama rine su "MAN yanzufa ba lokacin tunani bane mafita ya kamata mu nema... Waye ya kamata mu samu da zata zauna da MAMA?" Shiru BB yayi ya kasa magana zuwa wani lokaci cike da jimami ya fara magana "Irin abunda nayita fad'awa MAMA kenan lokacin da nake tambayarta danginmu... Yanzun ga irinta nan,waye zai zauna da ita a wannan halin?duk dad'in k'awaye bai kai d'an uwaba,amma MAMA tayi watsi da danginta da dangin mahaifinmu" Kallonsa kawai KHALEEL yake cike da rashin fahimta "Kamar yayafa dude?" Murmushi yayi mai ciwo kafin cikin jimami,takaici,haushi ya fara magana "Tun bayan dawowarmu garin nan daga DUTSE dai² da rana d'aya MAMA bata tab'a komawa garin nanba,y'an uwanta da suke ganin tana cikin rufin asiri zata taimaka musu,k'arshe duk wanda yazo sai dai ya koma yana k'unar zuciya,saboda MAMA korarsu takeyi bayan ta ci musu mutunci" "To amma duk da haka MAN ya kamata mu hanzarta nemo wanda zai zauna da itan" Duk sunyi shiru sun kasa tsai da matsaya akan wanda zasu samu ya zauna da MAMA a wannan yanayin da take tsakanin *RAYUWA DA MUTUWA*......... *~Fan's ku taimako da d'an jinya,kunga dai MAMA ta koma.... Please ba don halinta ba..~* 😤😤😤 *_~TEAM KHUBRA.~_* *~REAL SMASHER.~* 💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *28/ʝųŋɛ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* _Gaskiya na yarda kamar yadda kukayi alk'awari na gani kuma na tabbatar,babu abunda zanyi na saka muku face ci gaba da posting a duk lokacin da Allah ya bani ikon yin hakan,ina godiya kuma naji dad'in comment's enku.._ _Saboda haka zamu ci gaba daga inda muka tsaya in sha Allah SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV da kuma AUFANA suna tare da ku a ko wane lokaci kuma zamu ci gaba da tafiya tare,Allah ya bar k'auna da zumunci..._ _jinjina ga d'aukacin group's en_ *SMASHER & HUBBEEY NOVEL'S GROUP 1 & 2.* *SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVELLA* *SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE COMMENT'S ONLY* *MUSLIM LADIES WW* *SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE KITCHEN* *BARRISTER ALEEYAH & MUHIBBAT NOVEL'S* *SAWWAMA NOVEL'S* *LEEMA NOVEL FAN'S* _Allah ya bar zumunci da k'aunar junah..._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *3⃣6⃣* *K* allon da taga BABA ZUWAIRA nayi mata ne yasa ta gimtse dariyar tata,tana d'an murmushi ta k'arasa kusa da ita ta zauna tana dafa k'afarta "Allah kuwa BABATA ina cin abinci dayawama bakiga nayi kiba ba,kuma nayi k'arfi.... Kallifa kiga yadda nake iya d'aukan wad'annan robber en" Kallonta kad'ai tayi ba tare da ta iya maganaba saboda yadda taga ta hak'ik'ance akan maganar ne yasa tayi murmushin yak'e wanda akance "yafi kuka ciwo"... Kafin ta samu k'arfin guiwar yin magana "Kayya dai KHUBRA wannan ba bigiren k'arfi bane,banda abunki ina kika tab'a ganin mace tayi irin wannan sana'ar? Baya ga hakama su kansu mazan bakiga yadda suke wahalaba,kuma duk da haka ba kowa ne yake juran wahalar da wannan sana'a take da ba.. Ni kaina dan dai tun farko ina tsoron rasa ki,abu na biyu kuma tausayinki da rashin sanin hannun da zaki fad'a yasa ban musanta miki sana'ar nan da kika ce ita kike so... Amma har ga Allah wannan sana'a bata kwantaminba"... 'Dan murmushi tayi ba tare da ta sake cewa komai akan abunda BABA ZUWAIRA ta fad'aba ta hau fad'in "BABA bani abinci naci sai na tafi kinga dama ban shirya da wuriba,kada rana ta yimin a hanya" Itama BABA ZUWAIRA ganin KHUBRA ta bagarar da maganar yasa tayi shiru bata sake cewa komai ba,saima abincin da ta mik'o mata... Duk wani motsi da abunda take yi tana cin abincin,idanun BABA ZUWAIRA na kallonta... Ita kad'ai tana cin abincin kamar bata so tana yi tana yatsina face enta kamar wacce akawa dole haka take cin abincin... Da kyar take iya had'iyan abincin kamar mai shan magani.... Kai BABA ZUWAIRA ta gizgiza tana kallonta da tausayawa,yau kam ta rasa dalili da yasa y'artata take wannan abun "Jikin ne yake damunki?" Tayi tambayar tana dad'a k'ureta da ido.. 'Dago idanunta tayi ta kalleta tana kad'a mata kai "Wollahi BABA kwana biyu ina jin jikina babu dad'i,kuma na yau sai nake ji yafi na ko wane lokaci" "Ayyaahh!sannu,amma toh me yasa kike son fita duk da bakya jin dad'i kam? Ina ganin dai yau kam ki hak'ura da fita,idan Allah ya kaimu gobe sai ki je ko?" Shiru tayi bata sake magana ba,har BABA ZUWAIRA ta gama shirinta,sai da tazo fita ta kalli KHUBRA "To ni dai zan fita,kuma abunda na fad'a miki d'azu kiyi zamanki a gida gobe idan Allah ya kaimu kya fita,kin ji ko?" "Toh BABA Allah ya kiyaye hanya,Allah ya bada sa'a" "Ameen"..... Ta amsa mata.... Har ta juya zata fita daga gidan ta juyo tana fad'in "Afffff!na manta kinga anjima kad'an zan aiko yaro ya kawo miki magani.... Me ma kikace yana damunki?dan na samu a sayomin a gurin d'an lafiya jari ennan" "Wallahi gaba d'aya jikina ke min ciwo,cikin k'ashina kamar ana saramin da adda".... "Ashsha!sannu y'ar nan Allah ya yaye miki kinji.... Ni na tafi sai na dawo"... "To Allah ya kiyaye hanya" "Ameen..." BABA ZUWAIRA ta fad'a tana mai ficewa daga gidan gaba d'aya..... 《《》》 Damuwar da yake ciki a yau ji yake kamar a kowane motsawar second k'ara masa ake yi... Duniyar tayi masa d'umi wanda ya rasa inda ya kamata ya sa kansa dan yaji sanyi.... Hannu yasa ya dafe kansa ta kowane gefe,inda KHALEEL ke zaune kusa da shi shima yayi shiru kamar wad'anda akace musu MAMA ta wula..... Shiru kowa da abunda ke damunsa,kome BB ya tuna yayi saurin mik'ewa "MALAM bani key" Wani kallo KHALEEL yayi masa na jeka na gaji da kai,kafin yayi masa magana "Me zaka yi da key kuma? ko nace ina zaka?" "Kaga kawai ka bani ina ruwanka da inda zani?" "Niko nake da ruwa da inda zaka... Kasan dai babu yadda za ayi na baka key yanzu koh?kana cikin wannan halin za kayi driven en ko me?" Tsaki yayi daga haka kuma bai sake kula shiba yayi shiru,sai kansa da yake juyawa side zuwa side.... ZUHRA dake tsaye ta kallesu tana shirin magana sai dai tana jin tsoron abunda zata fad'a kada taja BB yayi mata fad'a irin na d'azu... Har tayi shiru kuma ko me ta tuna ta sake kallonsu tana fad'in "YAYA KHALEEL dan Allah ka maidani gida babu kowa sai su HANEEF kafin MAMA ta farfad'o sai na samu nayi girki,nasan yanzu haka suna can da yunwa" Shiru babu wanda yayi magana,sai dai abunda ta fad'a yasa KHALEEL en kallon BB yaga ko zai yi magana... Ko tari baiba bare su sanya ran zaiyi magana,hakan da yayi yasa KHALEEL mik'ewa yana yin gaba,itama ZUHRA ta mara masa baya... Har sunyi nisa a tafiya,ya d'ago yana kallon gurin amma bai gansuba,hanya yabi da kallo can daga nesa ya hangosu,a hankali ya mik'e zuciyarsa duk babu dad'i... So yake yaje gida dan akwai abunda yake damunsa,shi yasa yayi saurin barin gurin.... Har sun isa gurin da sukayi parking motan ya iso,babu wanda yayiwa magana cikinsu ya bude back seat ya zauna had'e da jingina kansa da jikin seat en.... Motan shiru babu wanda yake iya cewa wani komai har suka isa gida...... 《《》》 Misalin k'arfe 9:00pm ASHNA ta farka,har lokacin gudu suke shek'awa kan titi basu sauraraba,kallon gefe da gefenta tayi ta kalli yadda duk suka wani kafeta da ido,uban tsaki tayi wanda yasa guy en dake gefenta ya kalleta cikin magana irinta k'auraye "Kee!ya dai?kinawa mutane tsaki" Bud'ar bakin ASHNA sai cewa tayi "Dallah ina ruwanka dani ko kaji na kulaka da zaka wani yimin shishigi?kun kama kun wani sato to waima gidan wace uwar zaku kaini?? Banzaye b'arayin y'ay'an mutane kawai.." Furucin da tayi ba k'aramin kaishi k'ololuwar b'acin rai tayiba,take ya d'aga hannu da niyyar kifa mata mari sai dai me,tun kafin hannusa ya sauka kan fuskarta ta matsa jikin BIGGY tana fasa k'ara... Kallonta BIGGY yayi duk ta cukuikuyeshi idanunta a runtse,kamar wacce za a zarewa rai.. Dariya gaba d'aya yaran nasa suka sa dan gaba d'aya drama'n da akayi suna jinsu,banda BIGGY da ya sake d'aure fuska yana hararan yaran nasa.. "Da Allah kuyiwa mutane shiru" Ko gama rufe bakinsa baiyiba suka shiga taitayinsu,kallon wanda ke kusa da ASHNA yayi "Ka maida hankalinka jikinka tun kafin ranka ya b'aci... Daga yau kada ka sake k'ok'oarin aikata abunda kayi niyya kaji dai na fad'a maka".... "Sorry OGAA hakan bazai sake faruwa ba" Juyawa yayi ya kalli ASHNA da take murgud'a ma yaron nasa baki ya sake juyawa yana kallon window.... Tafiya ta mik'a inda basu suka isa gidanba sai misalin 12:00am,babu wanda ya kulata duk suka fice suka nufi cikin gida... Sai BIGGY dake bayanta,haka ya tusata a gaba har cikin gidan,a ransa yake raya "anya kuwa zai iya hak'uri da chik ennan?"... Shi kad'ai yana biye da ita yana kallon yadda take tafiya duk motsawan da zatayi duk da ba wani jiki ne da itaba amma shi kam tafiya take da imaninsa... Ji yake kamar tayi ta tafiya yana binta a baya a haka har zuwa tsayin wani lokaci.... 《《》》 Bayan shigansu gidan suka tarar da babu kowa cikin parlor,kitchen ZUHRA ta wuce dan yin girkin da tace za tayi,nan ta bar su BB da KHALEEL... Jin shigowansu yasa su HANEEF,KHALEEFA da kuma FATAHIYYA fitowa zuwa parlor a tunaninsu tare da MAMA suka dawo... Sai dai fitowansu suka tarar da BB su biyu cikin parlor babu MAMA... "YAYA ina MAMAN take?" FATAHIYYA tayi tambayar tana yamutsa fuska alamun damuwa shimfid'e saman fuskarta... Tsawan da ya buga mata yasa tayi baya cike da tsoron yadda taga ya mik'e yayo kanta... Dank'ota yayi yana zare jajayen idanunsa "Dan uwarki ba kece fitinanniyar da duk kika jawo muka shiga wannan halinba"... Yadda ya matse mata wuya yasa KHALEEL yin sauri ya fiszeta daga hannunsa yana fad'in "Haba MAN me kake shirin aikatawa kenan? Please!! Dan Allah kabi komai a sannu mana kada ka k'arawa kanka wata damuwar" "Dan Allah ka kyaleni da wannan y'ar iskar yarinyar,idan ba saita musu zama akeba basa ganewa,gara na raunata ta ko zan samu zuciyata tayi sanyi" "Haba mana to idan ka hukuntata hakan zai dawo da MAMA yadda take ne?" A fusace BB ya bar gurin yana watsawa FATAHIYYA mugun kallon zamu had'u... Shigansa bed room en ya hau safa da marwa a d'akin ya rasa me yasa a y'an kwanakin nan yake fama da mugun zafin zuciya... Kansa ya dafe tare da fad'in "Ya Allah ka kawomin mafita" Zama yayi ya sake yin shiru,shi kad'ai kome ya tuna kuma ya sake mik'ewa da sauri ya shige bathroom.... Cikin k'ank'anin lokaci ya gama abunda yake yi ya fito duk abunda yaje yi yana yi ne cikin gaggawa,yana shirin fitowa KHALEEL ya shigo.. Binsa da kallo yayi a lokacin ne kuma kiran sallan Azhur ya katse su... Babu wanda yayiwa wani magana haka KHALEEL en shima ya shiga toilet en... Yana gama abunda zai yi ya fice daga gidan.... Fitowan KHALEEL ya tarar baya nan dama yayi tunanin haka tunda yaganshi yana gaggawan fita.. Da sauri-sauri KHALEEL ya shirya,cikin closet en BB ya bud'e wasu kayan ko amfani dasu ba ayiba,nan ya d'auki wanda yake ganin zai iya sawa a lokacin ya fice cike da gaggawa kada abunda yake tunani ya faru..... Tada sallah da yaji anyi dai² lokacin da ya fito shi yasa shi tafiya masjeed en amma zuciyarsa tana cike da damuwan Allah yasa KHALEED ba tafiyan da yayi niyya yayi ba,in dai kuwa haka ne an samu matsala babbama kuwa... Da wannan zullumin a ransa ya isa masallacin,sai dai yana shiga ya hangoshi a sahun gabansa.. Hakan da ya gani ne yasa shi yin hamdala ya dai²ta sahunsa da na kusa da shi ya kabbara sallah... After an idar da sallah suka fito,gida suka nufa KHALEEL ya kalli side en BB "Kafa sa naji tsoro wallahi dana fito ban ganka ba" "Ohh!ni wai kake magana akai? "To idan ba kaiba dawa nake?" "Na sani ko ba dani kake ba" Kai ya kad'a yana jinjina k'arfin hali irin na KHALEED da yake iya rainawa mutane hankali amma a fili sai ya bar zancen haka tare da sako zancen "Ya kamata fa muyi tunanin abunda ya kamata muyi tun kafin dare yayi... Zuwa yanzun yaci ace mun nemo wanda zai ringa kula da MAMA saboda jinya ce sai mun sami mataimaki.... ZUHRA yarinya ce baza ta iya jinyan MAMA ita kad'aiba,ko dan school ensu bai kamata musa musu ido ace baza su ba dan MAMA tana kwance.... Yawwa!! Gaskiya ina tunanina ya kamata mu nemo HAJIYA LAURA dan ita kad'ai take da masaniya kan b'atan ZUHRA da kuma sace ASHNA da akayi a safiyar yau".... A fusace BB ya kalle shi "Ina ruwana da wata ASHNA taita b'atama mana ni babu abunda zai d'agamin hankali.. Ai duk laifin MAMA ne ya jawo haka ta faru,kuma ina tabbatar maka da sakamako MAMA ta fara karb'a tun a duniya".... "Nasan da haka amma dai ya kamata kayi tunani hausawa suna cewa 'Hannunka baya tab'a rub'ewa ka yanke ka yar'.... Shirun da yayi yasa KHALEEL samun daman tunasar da shi abubuwan da yake shirin mantawa,a lokaci guda duk jikinsa ya dad'a yin sanyi,kana kallonsa zaka gane hakan a tare da shi veins en kansa duk sun bayyana ya dad'a zama quit da shi.... "Ya kamata naje" Abunda ya furta kenan da yasa KHALEEL binsa da kallon mamaki "Ina kuma kake cewa za kaje?" "KHALEEL baza ka ganeba amma ya zama dole na nemi sulhu da dangina haka kuma dole ne na shirya MAMA da danginta idan har ba so take ta tashi cikin wad'anda Allah zai yanke rahamarsa daga garesu ba" Kai KALEEL ya kad'a "Tabbas wannan shi ne abunda za kayi ka tseratar da MAMA daga fushin ubangiji da take ciki,Allah ya bamu ikon abunda mukayi niyya.... Amma taya ya zamu billowa lamarin tunda yanzun MAMA tana kwance cikin mawuyacin hali,dole dai ko za muyi tafiyar nan cikin kwanakin nan sai mun samo mai zama da ita" Tunanin hanyar da zasu bi BB yake dai² lokacin da suka shigo haraban gidan... "Ina ganin muje mu nemi shawaran UMMI kan wannan al'amarin,za ta fimu sanin abunda ya kamata" Sai lokacin KHALEEL ya tuna ashefa UMMI bata san ya fitoba,kuma gashi bai kirataba bare ta san halin da ake ciki.... "Innalillahi wa-inna ilaihi raji'un" Abunda ya fito daga bakinsa kenan da ya jawo hankalin BB kansa cikin dauriya yana fad'in "Lafiya kake kuwa?" "Inafa lafiya...wallahi na manta tun fitowarmu UMMI bata saniba Ina da tabbacin yanzun haka hankalinta a tashe yake tunda bana gida... Sannan kuma ban kirata na sanar da ita halin da ake cikiba" Cikin nuna damuwa yake maganar dan kuwa yasan idan har UMMI ta duba bata ganshiba tabbas hankalinta dole ya tashi musamman ta kira shi taji bata same shiba,a nan kam hankalinta sai yayi k'ololuwar tashi... Hannunsa yasa ya dafe kansa ya rasa me ya kamata yayi,haka kawai ya nufi inda yayi parking yana shirin yiwa motan key BB ya dakatar da shi "Amma dai ai ka jira mu tafi tare ko?" Kasa yin magana yayi sai k'ok'arin tada motan da yaci gaba da yi,shi kuma BB ya koma side en mai zaman banza ya zauna suka bar gidan..... 《《》》 Bai barta ita kad'ai ba har sai da ya dangana da ita da bedroom en da yake ganin nan ya kamata ya ajiyeta,sannan ya fito ya jaa mata k'ofa'n ya rufe ta waje... A parlor yaransa suka baje suna jiran dawowarsa dan suna ganin ogan nasu ya fad'a tarko,duba da ganin yadda ya kafe yarinyar da ido duk sai wani tsare gida yake... Fitowarsa yasa su shiga taitayinsu suna jiran jin me kuma yazo da shi a wannan karon... Sai da ya zauna tukuna ya kallesu yana fad'in "Kai kufa maida hankalinku jikinku,sannan kunga yarinyar nan baba so wani cikinku ya shiga harkarta... Kun dai gane abunda nake nufi ko?" Dariya suka sa dukansu wadda tasa ran BIGGY ya b'aci ganin suna neman maida shi wani sauna... Wani uban ashar ya k'unduma musu wanda yasa suka nutsu daga dariyar da suke "Wane irin iskanci ne zai sa ina magana kusani a gaba kuna dariya.... Wato ga wawa yana magana ko? Allah ya baku sa'a inga wani d'an iska ya shiga harkarta,wallahi saina fasa kan mutum da alburushi"....... *~Wayyoo 😱😱 Allah jin BIGGY ya ambaci alburushi ya matuk'ar firgitani da har yayi sanadiyyar da alk'alamina ya fad'o k'asa.....~* *~KEEP FOLLOWING....~* *~TEAM KHUBRA~* *_REAL SMASHER._* 💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *29/ʝųŋɛ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *3⃣7⃣* *U* MMI cikin parlor sai kaiwa da kawowa take abun duniya duk yabi ya dameta saboda rashin ganin d'an lelenta yasa ta shiga damuwa,musammanma yau da bata san inda ya nufa ba,ita dai tasan a tsawon tasowarsa bai tab'a fita irin hakaba ba tare da ya sanar da ita inda za shiba.... To amma yau kam me yasa ya mata haka,bayan rashin sanar da ita da baiyiba ya fice kuma sai kiransa take amma shiru... Babban tashin hankalinta bai wuce ganin yadda take kiran wayan ba a d'aukaba,wannan shi yasa ta shiga damuwa sosai... Tun safe har zuwa wannan lokacin hankalinta ya kasa kwanciya,zuciyarta sai kawo mata tunani take iri-iri wanda sam basu da dad'in ji... Dalilin da yasa ta shiga addu'ah kenan tana nema masa kariya daga mahalicci... Haka ta tashi tayi sallah,har ta idar ta gama addu'o'in da za tayi tana jiran ganin ikon Allah,duk jinta take cikin damuwa sosai da har ta kasa cin abinci.... Parlor'n shiru babu abunda ke tashi sai k'ira'ar SHEIKH-MANSHAWIIY cikin tashar nan ta SAUDI-QUR'AN... Ta yi shiru tana sauraron karatun sukayi sallama a bakin parlor'n had'e da shigowa,kowanne fuska babu annuri... Da sauri UMMI ta shiga fad'in "Al-hamdulillah!! SON ina ka shiga yau tun safe?kasa hankalina duk ya tashi sai nemanka nake... Ina kaje kam duk layukan wayankama suna shiga baka d'auka?" Shiru yayi yana dad'a yin k'asa da kai,sai shigewa bayan BB yake,kamar wanda yake tsoron fad'in abunda aka tambayeshi... Shiru UMMI tayi tana kallon ikon Allah tare da rik'e hab'anta... Wucewa BB yayi ya zauna saman cuitions en dake parlor'n,cikin sanyin murya yake gaida UMMI datake binsu da kallon mamaki... Ta k'asan idonsa yake kallon UMMI da take tsaye itama har lokacin bata zauna ba,kuma ta kasa barin gurin... "Wai daga ina kukema tukun duk kun wani yimin shiru kunk'i magana... Na tambayeka kai kuma kak'i bani amsa ko?" "Kiyi hak'uri UMMI wallahi uzuri ne yasa muka fita bamu sanar dakeba,amma in sha Allah bazai sake faruwaba" BB ya fad'a yana hararan KHALEEL da ya kasa zama,sai yanzu da BB yayi magana tukun ya matso kusa da UMMI.. "Allah UMMI ba da niyya nayiba matsala ce tasa muka fita bamu sanar mikiba,kuma daima lokacinfa bana jin kin tashi... Yawwa UMMI kin hak'ura ko?" Cike da shagwab'a yayi maganar yana had'e hannunsa alaman ban hak'uri... Murmushi tayi tana matsowa inda yake,ganin tana murmushi shima ya shiga murmusawa.. Kunnensa ta rik'e ta d'an murd'a kad'an... "Argghh!UMMI wallahi da zafi,zafa ki ciremin kunne,dan Allah kiyi hak'uri,nayi miki alk'awari baran sake ba".... Duk maganar yana yin tane dafe da side en fuskansa da ummi ta rik'e idansa a rufe.... Shikam BB yana zaune yana kallon ikon Allah.... Sakin kunnen tayi tana fad'in "Gobema idan ka tashi fita kada ka fad'amin kaji ko" BB ta kalla tana murmushi,sai dai yanayinsa kad'ai ta karanta tasha jinin jikinta kan yadda ta ganshi,zama tayi lokacin shima KHALEEL ya zauna yana murza kunnensa dan da alama har lokacin bai daina masa zafiba..... "KHALEED lafiya kuwa kake na ganka cikin damuwa,anya kuwa babu wani abu dake damunka"... Ta d'an yi shiru na wasu sakanni kafin taci gaba da magana,sai da tayi masa nasiha mai shiga rai da ta dad'a sanyaya masa jiki da har yake jin kamar zai yi kuka a lokacin.... KHALEEL yayi gyaran murya yana fad'in "UMMI gaskiya ba lafiyaba dan kam yau al'amura duk sun dad'a cakud'ewa"..... Nan ya kwashe komai ya sanar da ita daya faru a safiyar ta yau.... Salati take ta zabgawa ta dafe bakinta da hannu,sai juya zancen take tana kad'a kai.... Sun jima parlor'n shiru babu mai magana zuwa wani lokaci sannan UMMI taja ajiyan zuciya tare da kallonsu "Yanzun waye kuka bari a gurinta?" Kallon-kallo suka shiga yi tsakanin su biyun,basu bata amsaba sai da ta sake mai²ta musu tambayan... "Amm!UMMI ai babu kowa gurinta yanzun muma dawowarmu kenan,ZUHRA kuma tana gida mun barota za tayi abincin da za a tafi da shi hospital en" "Too!Amma kuma labarin ita ASHNA fa ina fatan dai kun sanar da hukuma halin da ake ciki ko?" BB ne ya shiga kad'a kai alamar a'a,har za tayi magana KHALEEL ya tari numfashinta "Ehh!UMMI na sanar da D.P.O d'azun ta waya,amma lokacin naso ace zuwa muka yi,sai dai kuma muna hospital shi ne dalilin da yasa bamu jeba" "To Alhamdulillah tunda hukuma sunsan da b'atan nata,ammafa ni wannan al'amari yana d'auremin kai... B'atan y'an mata biyu lokaci guda,kuma tazaran sace ta farko da ta biyu duk a cikin shekara d'aya... Kaiii!Allah yayi mana magani,ubangiji ya tseratar damu daga sharrin masu sharri" Duk suka amsa da amin,sannan KHALEEL ya gyara zama yana shirin korowa UMMI labarin abunda ya kawosu a yanzun... "UMMI to amma mufa zuwa mukayi ki samo mana wacce zata zauna a asibitin,wa kike tunanin zamu samu ya zauna da MAMA? Ina nufin kisa a samo wata matar da zata yi jinyan MAMA har zuwa lokacin da zata samu sauk'i... Kinga ko da biyanta nema sai ayi idan zamu samu hakan" Yayi shiru yana jiran jin amsan da zata bayar... Murmushi tayi irin nasu na manya duk da bana tsammanin zata wuce 45 year's... "Lallaima yaran nan wato kuna so a samo wata matar daban tayi jinyar MAMA ko?" Shiru babu wanda ya iya amsawa saima kallonta da suke suna kuma kallon junansu.... "Ina ganin babu buk'atar nemo wata mata da zata yi wannan aikin,ni aikin me nake da ya wuce zaman gida tunda Allah yasa DADDYNKU baya nan bari na kirashi na sanar masa halin da ake ciki sai mu wuce,yanzun babu kowa a gurinta bai kamata a bar mara lafiya shi kad'ai ba,ya kamata ace mun hanzarta sai na kula da ita zuwa lokacin da Allah zaisa ta samu sauk'i... Daga nan kuma sai ku koma gida ku d'aukomin su ZUHRA da kayansu,bai kamata ace an barsu su kad'ai a cikin gidaba tunda ba wani girmane da su ba,ni zan kula dasu zuwa lokacin da HAJIYAN zata samu sauk'i,in sha Allah kuma zan kula da HAJIYAN,Allah ya bata lafiya mai d'orewa... Su kuma Allah ya bayyana mana inda suke idan da rabon mu sake had'uwa da su"... Ta k'are maganar fuskarta da annuri shimfid'e samanta Suma maganar ta UMMI kam tayi musu dad'i sosai wanda har suka rasa bakin magana... Cike da jin dad'i sukema UMMI godiya cike kuma da jin dad'i mara misaltuwa..... "To amma UMMI akwai fa wata sabuwar matsalar" KHALEEL ya katse musu maganar da suke dai² lokacin Da mamaki take kallonsa "Matsala kuma ta me kenan?" Bayanin tafiyar da zasu yi zuwa DUTSE suka yi mata da manufar da zata kaisu... "To amma yaushe kuka shirya yin tafiyar?" Tayi tambayar tana son sanin lokacin da suka yanke tafiyar "UMMI ai mu da a gobema muke son tafiya,tunda dai ance da sanyin safiya ake kama fara koh??" "Gaskiya ne to Allah ya biyaku da samako mafi kyau kan wannan niyyar taku" Taji dad'i sosai da bayanin da sukayi mata ta kuma yi musu fatan alkhairi cikin abunda zai kaisu,da addu'o'in samun nasara,daga haka ta mik'e ta shiga shirin tafiya hospital gurin MAMA...... 《《》》 ZUHRA har ta gama abunda za tayi a kitchen en ta fito,babu kowa cikin parlor sai FATAHIYYA kad'ai dasu HANEEF... "Ina su YAYA KHALEEL suka shiga kuma?" Tayi tambayan tana jiran jin amsan da zasu bata... FATAHIYYA kam kasa magana tayi dan da ganin alamu taji matsa a gurin BB.. Rik'on da yayi mata bana wasaba,shi yasa har yanzun tana nan tana faman murza wuyanta,danma Allah ya taimaketa KHALEEL na gurin ya kai mata d'auki da kam sai tafi haka jin jiki.... "YAYA ZUHRA sun fita,amma kamar dai masallaci suka tafi" "To ama kuma idan masallaci ne ai ya kamata ace zuwa yanzun tuni sun dawo tunda gashi har ana sallan la'asar nefa" "Amma YAYA ZUHURA bakya ganin ko sun jira suyi la'asar enne kafin su dawo" KHALEEFA ya fad'a "Ehhh!to kumafa haka ne.... Maza kuje kuyi sallah kuzo kuci abinci kunji ammafa ayiwa MAMA addu'ah kunji ko?" Cikin sauri suka tashi suka nufi yin sallah,da yake sun san warning en da BB yayi musu kan rashin yin sallah,idan aka bashi labarin ba suyi sallah ba su da shi... Shi yasa tana yi musu magana suka yi saurin tashi dan yin sallah.... Bayan lokaci mai tsayi suna zaman jiran BB ya dawo dan tafiya hospital en,amma shiru har bayan salla'n Maghreb.... Sai bayan da aka idar da sallah'n ishaa sannan suka shigo gidan shima a gurguje suka shigo,nan KHALEEL yayima ZUHRA bayani dan shi kam BB ko tsayawa baiyiba ya shige ciki... Haka suka shige kowa dan had'a kayan da yake buk'ata sannan suka fito lokacin KHALEEL har yayi waje,a parlor BB ya tadda su nan ko ya tsaya kansu fuska a d'aure ya jaa musu kunne kan duk wanda aka ce masa yayi wani abu na badai-daiba to ya kuka da kansa dan kam zaima yaro hukunci dai-dai da abunda yayi... Jikin FATAHIYYA ya sake yin sanyi dan ita kam tana tunanin wannan fad'an na BB da ita yake ba kowaba shi yasa ta dad'a sunkuyar da kanta k'asa uwa wata munafuka... Har suka bar gidan babu wanda yake k'wak'wk'waran motsi cikin motan haka suka isa gidan su KHALEEL inda zasu soma sabuwar rayuwa da babu MAMA cikinta...... 《《》》 'Dakin take k'arewa kallo tana yamutsa face,ko gama shiga d'akin bata yiba ta ji an rufe k'ofan d'akin... Tab'e baki tayi taci gaba da abunda take na daga yamutsa fuska haka har ta isa bakin mirror en d'akin... Kan stool en gurin ta zauna tana d'ora kanta kan k'afarta duk ta wani takure kamar wacce take jin mugun sanyi... Kusan awa guda bata ji motsin kowaba hakan yasa ta sauka daga kan stool en saboda ta gaji da zaman gurin.. Can wani space da ta gani tsakanin closets da bango ta shige ta dad'a takurewa sai yanzun data ga dare yayi sosai wani tsoro ya shigeta duk tunanin gida da MAMA shi yafi damunta,ko wane hali su MAMA suke ciki da sukaji labarin an sace ta... Wannan tunanin da tayi shi yasata sa kuka mai tsuma zuciya tana yi tana surutai ita kad'ai "Wayyoo!!! ni shi kenan bazan sake ganin MAMA ba da su ZUHRA,wayyoo!!! Allah sun sace ni ba zasu sake barina naga MAMANA ba" Tana tsaka da kukan aka turo k'ofan had'e da shigowa,dube-dube ya gamayi cikin d'akin amma bai gantaba kuma dai ya tabbatar da ya kulle d'akin tana ciki.... K'arasa shigowa yayi cikin d'akin bayan jiran da yayi da magana yaji shiru,ya nufi door en toilet amma wayam babu kowa... Can tsakanin closets da bango ya hango k'afafunta da yake d'akin akwai haske,gurin ya nufa yana mamakin me kuma take yi a nan? K'arasawa yayi gurin da take da niyyar yin magana sai dai me tun kafin ya isa ya fara jiyo kukanta da ba'a ji sosai sai an matso kusa da ita... "BEAUTY me ya sameki kike kuka?"...... ~Tofa wata sabuwa inji y'an chacha,su ASHNA kuma an koma BEUTY ammafa ba a bakinaba a bakin BIGGY~... 《《》》 "Haba KHUBRA me kuma ya kaiki kwanciya da wannan al'murun ke dama da ba lafiyaba ai sai ki jaa jikin naki ya dad'a yin zafi" Shigowar BABA ZUWAIRA kenan gidan ta tarar da KHUBRA kwance tsakar gida saman tabarmar kaba.... 'Dan d'ago da kanta tayi kad'an ta kalli BABA sannan ta sake maida kanta ta kwantar saman hannunta da tayi matashi da shi. "Sannu da dawowa BABA" "Yawwa y'ar nan,kinga na ce zan aiko miki da magani shiru gashi da gani jikin naki ke damunki... Yau kam ISAH bai fito da wuriba shima sai yanzu da zan taho na biya naganshi... Shi ne yake shaidamin gona yaje dubawa,Allah dai ya taimaka na samo miki maganin,yi maza ki tashi ki sha kinji idan aka jima an yi sallar ishaa sai ki kwanta kinji ko,Allah dai ya baki lafiya" Duk maganar nan da BABA ZUWAIRA ke yi hankalin KHUBRA ba a kanta yake ba,tunani ne iri² duk zuciyarta ta cunkushe,jinta take a wannan lokacin tana so tayi kuka ko zata samu sauk'in rad'ad'in dake damunta a zuciyarta,a cikin kwanakin nan tana yawan yin mugayen mafarkai da wani mutum da har zuwa yanzun ta kasa tantance waye ne,sai dai duk lokacin da zata ganshi cikin muguwar damuwa take ganinsa wannan dalilin da yasa mafarkin ya tsaya mata a rai,yawan mafarkin da take da shi yasa ta shiga damuwa da ta haddasa mata ciwon jikin da take fama da shi cikin satin.... Sai da BABA ZUWAIRA ta tab'ata sannan ta tashi ta zauna had'e da karb'ar maganin tana juyashi a hannunta... Da kyar ta samu tasha maganin sannan ta tashi da nufi yin sallah.... Tun misalin k'arfe 8:30pm tayiwa BABA ZUWAIRA salamma ta shige d'aki,ita ko BABA'N a lokacin tunaninta duk jikin ke damunta,ta dai bita da fatan samun sauk'i fuskarta duk alamun damuwa da halin da y'ar tata ke ciki... Ko da ta shiga d'akin bayan ta kwanta nan ta shak'i kukanta har ta godewa Allah... Sai bayan ta gama kukan ta tsaya tunanin menema wai yasata kuka haka? Tana wannan tunanin bacci ya d'auketa cike da mafarkai iri-iri.... 《《》》 Gari na wayewa suka hau shirin barin garin,misalin k'arfe 10:00am suka yiwa UMMI sallama suka mik'i hanya bayan d'umbin nasiha da suka sha a gurinta sannan ta musu fatan dawowa lafiya... Sai da suka biya suka ga jikin MAMA,sai daifa har zuwa wannan lokacin MAMA bata sanma wanda yake kanta ba,bare ta samu damar yin magana..... Daga nan suka d'auki hanya sai garin na JIGAWA DUTSE...... 乛乛乛乛乛 Safe trip BB and KHALEEL..... *~TEAM KHUBRA.~* *_REAL SMASHER._* 💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *1/ʝųlყ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* _Matso maza kuji mutanen arziki,wollah a duk inda kuke ina k'aunarku irin wacce bazata fad'uba kuma ina alfahari daku_ *MISS ABATCHA,ZAINAB (ZEE MA'DAGWAS & KHADIJA (FRESH KHADEEY)* _Kuyi komai ba komai mutanena Allah ya bar k'auna....*ME LUV U* ❤ irin tottaly ennan..._ *~__________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *3⃣8⃣* *T* afiya ta mik'a a b'angarensu BB,inda babu wanda ke wata magana hakan ne yasa tafiyan nasu ya zama kamar na kurame... K'arfe 1:15pm Motansu ya parker k'ofar wani madaidaicin gida,ginin gidan dai² na talaka dake cikin rufin asirin ubangiji,a cikin garin na DUTSE unguwan shiru babu hayaniya,fitowa BB yayi ya tsaya yana tunanin ko ina ne gidan daga cikin jerin gidajen?... Sun shafe tsawon lokaci suna jira a gurin ba tare da ganin kowaba,sai zuwa can wani d'an dattijo ya fito daga zauren d'aya daga cikin gidajen,da alamun shima kamar gona zai tafi duk da wannan tsufan nashi... Ganin mota tsaye bakin k'ofar gidan ya d'an kalli motan da mamaki a tare da shi... Da sauri KHALEEL ya kalli BB "MAN ya kamata fa mu tambayi wannan datijjon tun kafin mu rasa wanda kuma zamu tambaya" Kallonsa BB yayi tare da murmushin k'arfin hali,sannan ya sake bud'e motan motan karo na biyu ya fita cikin sauri.. Matsowa yayi kusa da dattijon yayi masa sallama fuskarsa da fara'a,shima dattijon ya mayar masa da murmushin tare da amsa masa sallaman da yayi masa... Bayan BB ya gaida shi ya amsa masa,sai kuma shiru ya ratsa tsakaninsu,tunanin BB ta ina zai fara masa bayanin abunda ya kawosu,shi kuma dattijon yana kallonsa ne irin na rashin sanin nan... "Samari daga ina haka?sai dai kuma ban shaida kaba" Sai da BB ya sake yin wani murmushin kafin ya fara magana "BABA daga kano muke,to dama akwai wani gida da muke nema kuma dai gaskiya BABA gidan ne ya b'ace mana,saboda shekarun da yawa" Murmushi dattijon yayi irin nasu na manya kafin ya tambayi BB "'Dana wane gidane kuke nema haka?" "Ehhh to BABA gidan MALAM ABDU MAI AL-MAJIRAI muke nema,ko nan ne unguwan da yake?" Murmushi dattijon ya sake yi masa tare da gizgiza masa kai "K'warai kuwa nan ne unguwan da yake gama gidan da kuke nema nan kusa da kai" Ya fad'a tare da nuna k'ofar gidan da ya fito yanzun "To amma wa kuke nema a gidan shi kuke nema ko wani daban kuke nema?" Sosai BB yaji dad'in samun gidan da suka yi ba tare da sun sha wata wahalaba,fuskarsa d'auke da jin dad'in hakan ya furta "BABA yana raye ne ko kuwa?" "Sosaima kuwa d'an nan,sai dai ya jima yana jinya dan a halin da ake cikima yana kwance ne sai dai a tayar da shi saboda k'afafunsa da suka samu matsala" "Eyyyahhh!Allah ya bashi lafiya.... Amma BABA idan da hali muna son ganinsa ne dan shi muka zo garin nan" "To to kada ka damu yaro,bari na shiga na sanar masa da yana da bak'i tukuna" Da sauri BB ya amsa da ‘’To BABA mun gode sosai‘’ Sai da ya ga shigan dattijon tukun ya juyo,ta saitin window en da KHALEEL yake ya tsaya tare da knocking.. Sauke glass en yayi yana kallonsa "Yahh!ina fatan dai munyi nasara" "Sosaima kuwa Allah ya taimakemu wollahi,ashema a k'ofar gidan muka tsaya" "Kaiiii!ammafa naji dad'i sosai wollahi,to amma KAKA yana raye kuwa?" Sai da yayi wani k'ayataccen murmushi kafin ya amsa "K'warai kuwa,sai dai kuma ance bashi da lafiya yanzun hakama" Yanayinsa ya d'an sauya lokacin da ya fad'i hakan,shima KHALEEL en yanayin da yake kan fuskarsa kenan lokacin da yaji hakan... "Allah dai yasa ba wani seriuos ciwo ne da zaisa ya kasa fuskantar dalilin zuwanmu ba" KHALEEL ya fad'a yana sauraron yaji me BB zai ce kan hakan.. "Ameen kam dan wallahi har murnan da nake ya soma b'acewa,gaskiya ina cikin damuwa yanzun haka da naji wannan maganar" "Tohh!Allah yasa dai babu wani abu da zai mayar mana da farin cikinmu baya" Suna cikin maganar dattijon ya fito yana waigawa yaga ina saurayin ya nufa kuma,bayan ya barshi tsaye a k'ofar gidan.... A jikin motan ya hango shi ya jingina,k'arasowa yayi da murmushi a fuskarsa "To samari zaka iya shiga yana sauraren zuwanka" Kallon KHALEEL yayi da yake k'ok'arin fitowa daga motan,sukama juna murmushin k'arfin hali sannan sukabi bayan dattijon zuwa cikin gidan.... Mata ne da k'ananan yara wad'anda bazasu iya aikin gonaba sunata aikace-aikace a tsakar gidan,gaisuwa kam su BB sun shata musamman da aka gansu da shiga data bambanta da yanayin y'an garin... Haka sukaita wucewa har suka isa turakar mai gidan,shigansu suka tarar da wani DATTIJO da yafi wanda ya rakosu tsufa a kwance k'afafunsa sun kumbura sosai suna tsatstsafar da ruwa ta jikinsu... Da tausayawa suke kallonsa wanda duk mai raunin zuciya idan ya kalli k'afafun sai yayi masa hawaye,inda tafin k'afar tasa yayi wani irin sai wata irin sab'a yake kamar jikin maciji..... Kallon yanayin da yake ciki yasa jikinsu dad'a yin sanyi,dan har sun yanke tsammani da cewa wannan dattijo zai gane duk wani bayani da zasuyi masa a wannan lokacin,sai dai kuma maganarsa ta basu mamaki matuk'a... "Marhaban lale" Juyawa sukayi suka kalli juna da mamaki,sannan kuma suka kalli dattijon dake kwance... Guri suka samu suka zauna,nan dattijon da ya rakosu shima ya samu guri ya zauna daga gefen wannan dattijo dake kwance... "Samari daga ina haka?ban shaida fuskokinkuba" Sai da suka sake kallon juna sukayi murmushi tukun BB ya juya ya kalli dattijon tare da fad'in "BABA mu bak'i ne daga garin KANO,sai dai kuma ba lallaine dama ace ka ganemu ba" K'ura masa ido dattijon yayi da alama akwai wani abu da yake son karanta akan fuskarsa da har yasa yake masa irin wannan kallon k'urilla,yanayin kallon da yake masa ne yasa shi yin shiru yana binsa shima da ido had'e da murmushi... "Yaka nan zo maza,matso kusa dani kaji zo?... Ina ji ajikina wannan yaron duk inda ya fito jini nane shi duk inda ya fito" Da mamaki suka sake kallon juna shi da KHALEEL,inda KHALEEL en ya d'aga masa kai alamar yaje gurin dattijon... Matsawa yayi kusa da dattijon,shi kuma sai k'ok'arin mik'ewa yake ya zauna,da sauri d'aya dattijon da ya rakosu ya mik'e ya kamashi ya zaunar... Hannunsa ya mik'a ya rik'o BB yana dad'a kallonsa... "Tabbas ko tantama babu wannan yaro duk inda ya fito jinin SAFWAN ne.... Allah sarkin hikima,yaro ina ka baro SAFWAN en? Yana raye ko kuwa ya mutu ne? Iya tsawon wannan lokaci SAFWAN ya watsar damu sam yak'i zuwa ya ganmu duk tsayin wad'annan shekaru,ina ya shiga haka?" Ganin bai bashi amsaba yasa shi sake fad'in "Yaro ka sanar dani ko dai da gaske SAFWAN en ya rasu kamar yadda nake mafarki?" A lokacin da yayi wannan maganar idanunsa har sun kawo ruwa,wanda suke shirin zubowa,saboda rashin sanin amsar da za a bashi... "A'a BABA yana raye" BB ya fad'a wanda fad'ar hakan yasa KHALEEL ya kalleshi,zuciyarsa cike da tunanin ‘’Too kaji mutumin nan yana neman b'allo mana ruwa,idan har ABBA yana raye a wane bigere yake rayuwa,ko kuwa yasan inda ABBAN yake da har ya fad'i haka?‘’ Saurin katse tunaninsa yayi ya sake maida hankalinsa kan abunda BB zai fad'a... "Too Alhamdulillah da har kuwa yana raye,amma me ya faru tsawon wannan shekaru ya kasa zuwa ya ganmu bayan yasan muna raye kuma muna cikin garin nan,idanma ace bana raye shin ba ga y'an uwansa nanba da suke ciki d'aya,ko kuwa shi kenan ya yanke zumunci da mu?" Jin maganar BABA ABDU yayi kamar zubar wuta a jikinsa,cikin zuciyarsa yana jinjina kalaman da zai sanar da BABA a wannan halin da yake.... Sai da BB yayi k'arfin hali sannan ya fara magana,duk wani labari daya shafesu tun daga barin garin har zuwa wannan lokacin da yake zaune a gabansa bai b'oye masaba ya sanar da BABA ABDU,amma banda labarin b'atan ASHNA... Al'ajabi da mamakin abunda ya faru cikin labarin da BB ya sanarma da BABA ABDU yasa shi kuka yana fad'in ‘’Lallai wannan al'amari daya faru tabbas muk'addari ne daga Allah,Allah ya tsara haka sai ya faru daku a rayuwarku,babu kuma wanda ya isa ya tsallake K'ADDARA..... To amma ina ita mahaifiyar taku da sauran y'an uwanka da kace suna nan? A wane hali suke yanzun?kuna tare gaba d'aya a guri d'aya ko kuwa?" Duka tambayoyin BABA ABDU ya jerowa BB ba tare da ya jira ya amsa wasu ba.... "Ehh!BABA muna tare dasu can garin kano,sai dai kuma ita mahaifiyar tamu a halin yanzun bata da cikakkiyar lafiya,wanda ta kaiga har bata iya shaida wanda yake kanta" "Subhanallah!wannan wane irin ciwone haka ya sameta?" "BABA muma dai gaskiya bamu san wane irin ciwo bane,tun da likita ya shaida mana suna buk'atar ganin wani babba daga zuri'ar mu dan suyi magana dasu,to mu kuma babu kowa a tare da mu,shi yasa muka yanke hukuncin nemanku mu sanar muku halin da muke ciki".... Dattijon dake gefe ne ya mik'e tsaye cikin fushi "Wato da can baku neme muba sai yanzu da al'amura suka gama cukurkud'e muku kuka lallab'o gurinmu.... To kuma tashi ku d'ebi tsummokaran jikinku ku k'ara gaba mu ba abunda zamu iya yi muku a halin yanzu,muma fama muke da namu mahaifin kun dai ga halin da yake ciki... Saboda haka maza ku tashi ku koma babu abunda zamu iya yi muku a halin yanzu,ita mahaifiyar taku zata iyayi muku komai ai na rayuwa ciki kuwa harda samar muku wasu dangin uban‘’.... Jikinsu duk yayi sanyi da jin furucinsa,suna sauraron yadda yaketa fad'a.. Shi kuwa BABA ABDU yana zaune yana kallon ikon Allah yadda d'an nasa yake ta fad'a kamar zai ari baki... Murmushi yayi ya sake kallon d'an nasa da ya kasa yin shiru har zuwa lokacin,ganin bai gane me shirun nasa yake nufiba ne yasa shi yin magana "Ya isa haka KHALEED" Kallon-kallo sukayi tsakanin KHALEEL da BB,sannan kuma suka juya suka kalli mutumin dake fad'a ganin yayi shiru a lokacin,suka sake kallon BABA ABDU... "Banda abunka KHALEED ina kai ina fad'a ga wad'anda basu da laifi?ko ubangiji idan muka masa laifi yana hak'uri damu ya kuma gafarta mana.... Kuma ubangiji baya tab'a kama bawa kan laifin da ba nasaba" "Kayi hak'uri BABA raina ne ya b'aci shi yasa‘’ 'Dan murmushi yayi sannan yayi gyaran murya "Allah sarki MURJA Allah ya bata lafiya,shi kuma SAFWAN idan yana raye Allah ya bayyana mana inda yake" Gaba d'ayansu suka amsa da ameen... "Da gani dai wannan da yake zaune kusa dani shu ne KHALEED ko?" KAKA ya tambaya yana murmushi shima,duka suma suka murmusa tare da amsa masa,juyawa yayi ya kalli KHALEEL "Shi kuma wannan abokin nawafa? Ya tambaya yana y'ar dariya "KHALEEL suna na KAKA" "Ahhhh!IBRAHIM KHALEEL kenan... To Allah ya muku albarka da kuka zo nemanmu bayan lokaci mai tsaho"..... "KHALEED kasa a kira sauran y'an uwanka da mutanen gida yanzu ina son ganinsu" BABA ABDU ya fad'a yana kallon d'ayan dattijon dake tsaye har lokacin,da sauri ya fita don aiwatar da sak'on BABA.... Bayan wucewar wani lokaci cikin turakar ta d'inke da jama'ar gidan manya da yara kowa ya matsu yaji me BABA zai sanar musu haka mai muhimmanci da ya tarasu gaba d'aya.... Sai da yayi gyaran murya yana jingine jikin pillor sannan ya kallesu d'aya bayan d'aya ya fara da fad'in "Alhamdulillah da Allah ya nunamin wannan rana da na jima ina sauraron zuwanta a tsayin rayuwata... Dalilin daya sa na taraku a nan ba komai bane face sanar daku wani muhimmin al'amari game da SAFWAN da iyalinsa,wanda wasu daga cikinku sun sanshi wasu kuma basu saniba"...... Take BABA ABDU ya jaddada labarin SAFWAN da iyalinsa ya sanar dasu da duk wani abu daya faru dashi bayan barinsa garin kamar yadda BB ya sanar da shi,yana gama basu labarin turakar tasa kowa dake ciki ya d'auki salati,masu kuka nayi masu jinjina lamarin nayi... Bayan wani lokaci aka samu kowa yayi shiru sai jimami da kowa keyi da abunda ya faru... BABA ABDU ya kalli BB dad'an murmushi a fuskarsa yake fad'in "Kaga wannan?" ya nuna dattijon daya rako su d'azun "Sunan sa KHALEED shi ne babba cikin y'ay'ana,sannan wannan shi kuma sunansa SULAIMAN,sai kuma wannan AYUBA kenan,sannan sai mahaifinka,daga shi kuma sai k'anwarsu da ta rasu shekaru bak'wai da suka wuce wato FALMATA"... Wad'annan kuma ya nuna matan dake gefensa matansu ne,haka yayita nuna masa su d'aya bayan d'aya yana gabatar dasu a gurinsa,sannan shima ya gabatar da shi a matsayin d'an uwansu da basu saniba sai wannan lokacin.... Hira sosai tsakanin mutanen parlor'n anata dad'a gaisawa,sannan BABA ABDU ya sallamesu kowa ya fice aka barsu daga shi sai su BB zaune cikin turakan nasa... Nan da nan aka tashi girki na musamnan a gidan saboda zuwansu,tarba da karamci kam sun samu gurin mutanen gidan wanda basu tab'a tunanin samunta daga gurin mutanenba..... *2 DAY'S LATER.* Kwanaki biyu kenan da zuwansu garin wanda suke sa ran a washe gari za suyi haramar barin garin idan Allah ya kaimu ko dan sanin yanayin da jikin MAMA yake a halin da take ciki ko an samu ci gaba ko kuma akasin haka Allah shi ne masani... Farin ciki kam suna cikinsa tun daga zuwansu garin har zuwa wannan lokacin,kullum cikin hira suke da KAKA da kuma su BABA KHALEED suna dad'a basu labarin zamansu da ABBANSA,wani abun idan sun fad'a sai dai suyi dariya wani ko har da k'walla saboda rashin tabbas akan ABBA'N yana raye ko akasin haka..... Yau tun safe suke shirin komawa KANO kamar yadda suka sanar da KAKA dama kwana 3 suka zo da niyyan yi.... Sai da ya had'asu yayi musu nasiha sosai kan su rik'e zumunci... Sunyi masa godiya tare da alk'awarin dawowa nan da wani lokaci ba mai nisaba... Sosai yaji dad'in hakan,sannan yayi musu alk'awarin da sun koma zai turo su BABA KHALEED suzo su dubasu... Sunji dad'i sosai da yadda aka karb'esu,sannan sukayi sallama dasu suka d'auko hanyan dawowa KANON DABO...... 《《》》 Kimanin kwanaki biyu (2) KHUBRA bata samu ta fita gurin sana'ar taba kamar yadda ta saba... Duk jikin ya takura mata da ciwo a kwanakin da yasa ta kasa fita,dalilin da ya sa BABA ZUWAIRA ta dad'a sa ido kenan kanta tana dad'a bata kulawa ta musamman saboda yadda take ganin jikin nata.... Yau ta tashi jikin da sauk'i sosai har tana iya yin komai da kanta.... Tashinta da sassafe ta share gidan ta gyara ko ina sannan ta shiga tayi wanka,ta fito kenan daga toilet en BABA ZUWAIRA itama ta shigo gidan d'auke da robber a kanta... Sororo ta tsaya kallonta tana kuma kallon gidan,dan tana da tabbacin ita tayi wannan aiki... K'arasowa tayi cikin gidan tana son yin magana... "Sannu da dawowa BABA" "Yawwa y'ar nan" Ta fad'a tana bin KHUBRAN da kallon mamakin yadda ta ganta,bayan a kwance ta barta ta yaya kuma yanzun zata ganta ta mik'e kamar ba itaba... "Sannu kin tashi?" "Ehhh!wallahi BABA,ai jikin da sauk'i sosai har ina jin yauma zan iya fita" Da sauri BABA ZUWAIRA ta katse ta tana fad'in "Haba haba KHUBRA me zai hana ki k'ara hak'uri zuwa jikinki ya sake warwarewa,in yaso sai ki fitan ko kuwa?" Cike da tab'ara irin ta y'ay'an fari kuma na k'arshe ta hau buga k'afa tana fad'in "Ni wollahi a'a ban yardaba,nafa samu sauk'i sosai" Kallonta BABA ZUWAIRA take tana sake bud'e ido tana kallon ikon Allah "To ai shi kenan tunda kin dage Allah ya bada sa'a,kuma Allah ya k'ara sauk'i kinji" Tsalle ta hau yi sosai tana ta murna BABA ta amince mata zata koma gurin sana'ar tata.... Cikin zumud'i ta hau shiryawa,yau da yake ita take son fitan bata b'ata lokaciba tayi ta gama shirinta,sannan tayiwa BABA ZUWAIRA sallama,dai² lokacin itama ta gama shirinta tana jiran al-majiran da zasu d'ibar mata kayan abincin zuwa bakin kasuwa.... Tafiya take cike da kuzari had'e da karsashi saboda yau kam tana jinta cikin k'oshin lafiya,sai dai d'an abunda ba a rasa ba da yake damun zuciyarta.... Har ta k'arasa bakin rafin ta d'ebo ruwa,ta kuma juyo don komawa cikin gari,tana tafe ta kare kanta da hat ta gargajiya saboda rana da ake tsulawa ga zafi..... Yayinda wani gefen na sararin samaniya ya had'a hadari wanda yake ta gangamowa lokaci guda har garin ya had'e,da alamun yau kam za a iya dacewa da ruwan sama.... Wani iska ne ya taso mai k'arfin gaske,wanda sakamakon haka yasa wasu daga cikin mutane suketa guje-guje,bayan k'uran ya lafane kuma wani iskar cike da yanayi mai dad'i ya sake tasowa... Cikin nutsuwarta take tafiya tana kuma ci gaba da tura kuranta ita d'aya a hanya.... Wani bak'in PRADO ne ya yanko kan kwaltan da mugun gudu sosai,dai² kafin motan ya k'araso inda take aka tsaya,tare da jan brake da k'arfi wanda ya bada wani mugun sauti ji kake KUUUUUUUUUUUU!!!............... *_~KEEP FOLLOWING.....~_* *~#TEAM KHUBRA.~* *_REAL SMASHER._* 💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *2/ʝųlყ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* _Jinjina ga d'aukacin mabiya novel en *"Y'AR GARUWA"* a duk inda kuke ku en masoyanane na hak'ik'a,ina godiya sosai da k'aunar ku gareni Allah ya barmin ku a duk inda kuka kasance ina al'fahari da ku.._ *~__________________________~* _Mun gani kuma mun yaba,danko hausawa na cewa "yaba kyauta tukuici" tabbas garemu muma hakan take,sanin masoyi sai Allah *CWEET LEEMA* muna godiya tare da jinjina gareki lallai ke d'in ta daban ce,ki jima kiyi k'arko a kullum kuma a ko ina SMASHER da HUBBEEY naki ne ke d'aya,Allah ya bar mana zumuncinmu daga nan har a Al-jannah muna fatan ci gaba da kasancewa tare.._ *~__________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *3⃣9⃣* *T* ana daga gefen titin tana ci gaba da tafiyanta wanda jin k'aran motan da tayi baisa tayi yunk'urin tsayawaba saima ci gaba da tayi kamar ta samu sak'on k'in tsayawar. Yanayin yanda garin yake ne ya bata damar k'ara sauri saboda wasu irin thunderstorm da ke tashi akai-akai. Tsayawan da motan yayi a dai² lokacin hakan ya farune sakamakon motan dake fidda hayak'i bayaga engine en motan da ya d'auki zafi,fitowa suka yi suka bud'e gaban motan ko dan su samu hayak'in ya sarara,wannan dalilin shi yaja musu tilas suka tsaya a gefen hanya'n. Bayan motan suka duba cikin irin galan da masu mota ke zuba ruwa saboda gudun ko ta kwana irin wannan a tafiya. Shiru sukayi suna kallon juna,saboda rashin ruwan a tare da su sannan suka kuma maida hankalinsu kan hanya'n da yarinyan nan tabi,can nesa dasu sosai suka hangota dan kam tsakaninsu da ita da tazara mai nisa. "MAN wai ya zamuyi ne kam kanafa kallon yadda garin nan yake dad'a had'ewafa kuma ka tsaya anan kana wani kallona" Harara BB ya bankawa KHALEEL dake magana,yanayin yadda yayi masa ne yasa shi shek'ewa da dariya,sai da yayi mai isarsa sannan ya kama hanya cikin sauri don tsayar da ita tun kafin ta b'acewa ganinsu. Cikin sauri yake bin bayanta wanda da k'yar ya samu ya isa bayanta a dai² lokacin da take k'ok'arin karkatawa ta shiga hanyan da zai sadata da cikin gari. Sallama yayi mata yana daga bayanta dan yasan hakan dai shi ne kad'ai abunda zaisa ta tsaya. Cikin sa'a kuwa ya samu ya tsaya tare da juyowa don ganin waye ne mai maganar duk da tasan hanyan babu mutane sosai,duba da yanayin da aka tashi da shi a garin. Idanu KHUBRA ta bud'e sosai ganin fuskar dake tsaye gabanta,tunani ta d'an tsaya yi kanta d'age a sama tana son tuna inda tasan fuskansa. Magana yake yi wanda sam ta kasa bashi amsa saboda yadda ta lula duniyar tunani,har sai da yayi magana da d'an k'arfi sannan tayi firigigit da dawo duniyar da take tare da fad'in "Ammm!kace mene?" Shiru yayi yad'an tsaya yana binta da kallon mamaki da kuma tunanin inda yasan mai wannan muryan,kallo sosai ya k'ureta da shi sai dai bai gano komai kan fuskartaba,dalilin daya katse shi kenan daga tunanin da yake. Yana shirin yin magana BB ya iso gurin yana fad'in "MAN lafiya ka zo ka zauna ka wani shanyani a jeji bayan kana ganin yadda garin yake" Shiru yayi lokacin da ya k'araso ya gansu tsaye suna kallon-kallo tsakanin su. Kallonsu yayi sun kafe juna da ido,a hankali KHUBRA ta maida kallonta kan BB da isowarsa gurin kenan,dad'a fiddo idonta waje tayi da sauri kuma ta maida kanta k'asa had'e da dafe chest enta jin yadda zuciyanta keta skipping kamar zai fito waje. Tun daga sama har zuwa k'asa BB yake kallonta a zuciyarsa yake magana "Ina nasan mai wannan kamannin?anya ko itance ko kuwa mafarkine nake yi?" Sake kallonta yayi da yadda take tsaye jikinta na vibrating da gani kasan akwai abunda ya bata tsoro wanda yasa ta shiga yanayi irin na rashin gaskiya haka,da sauri ya katse shirun ta hanyar magana da ya sasu kallonsa "Ammm!baiwar Allah taimako muke buk'ata" Ba tare da ta kalleshiba ta furta "Taimako akan me kenan?" Sake kallonta yayi yanzun kam ya samu shaida ta biyu da take bayyana masa hasashen da yake yi akanta,abu d'aya yake nema don tabbatar da gaskiyar lamarin. "Muna buk'atar ruwane zamu sa a mota,mun d'an samu matsala ne so motan yana can kan hanya" Har lokacin duk maganar da yake yi yana yine idanunsa na kanta,yayin da ita kuma duk take jinta a takure saboda yadda take jin idanunsu a kanta. KHALEEL ya koma kamar wani idol yayi shiru yana sauraren muryanta dake masa yawo cikin kansa,so yake ya tuna inda yasan wannan muryan,yayin da a b'angaren BB shima hakan take dan shi kam gani yake a yanzun yana da yak'inin itance da kashi 50%,babban abunda yasa bai gama amincewa da itanceba ganin yadda wannan take b'aka,ga yanayin suturan dake jikinta sannan ya tsinceta cikin yanayin da baya tunanin KHUBRA zata shiga. Duk sunyi shiru har sai da yayi k'arfin hali tare da danne zuciyarsa kan lallaifa wannan ba waccan KHUBRA'N da suke tsammani bace,kawai dai yanayin halittane da kuma su d'in da suke cikin yanayi na rud'u yasa suke ganin kamar itan ce da gaske. Kautar da tunanin yayi tare da fad'in "Amm!ina fatan dai ba zaki damuba dan da d'an tafiya tsakanin nan da gurin da mukayi parking" "A'a babu komai,muje kawai" Ta fad'a tana juya akalar kuran nata da niyyan komawa bayan garin inda suka bar motan nasu. A baya suka shiga binta tana tura kuran nata,duk wani motsi nata akan idanunsa hakan yake yana ankare da ita,suna tsaka da tafiyan ne wata matashiya ta taho kanta d'auke da robber yellow da alama daga rafi take ta gansu suna tafiya,kallon mamaki tabisu da shi kafin tayi magana "A'a KHUBRA ina kuma zaki nufa haka bayan kin d'ebo ruwan kike k'ok'arin komawa" Cak!KHUBRA ta tsaya a gurin kamar anyi pausing enta ba tare da ta k'ara one step forward ba. "Shi kenan HAFSAT kin tonamin asiri,wayyyo Allah ka kawomin d'auki" Abunda ta furta kenan k'asa-k'asa idanunta a runtse ba tare da tayi tsammanin wani cikinsu zaiji me ta fad'aba. A hankali ya furta "ALHAMDULILLAH ALAA KULLI HALIN! ALHAMDULILLAHIL-LAZIIY BI NI'IMATIHI TATIMMUS-SALIHAT!!!" Yanzun kam ya gama samun shaidan da ya bayyana masa itan ce dai wacce yake hasashe d'ari bisa d'ari yanzun ya tabbatar da hakan. "Amma to ya akayi ta koma haka ne kam?" Yayima kansa tambayan ba tare da tunanin samun amsa daga gare shiba. Matsawa yayi a hankali ya d'auke hat en dake kanta tare da sake k'ureta da kallo,ko tantama baya yi yanzun kam daya ga fuskarta ya gama yin amanna akan yak'ininsa gaskiya ne. "Why KHUBRA zaki nuna baki ganemuba a yanzun?me yasa?me yasa za kiyi haka??" Cike da tsawa ya k'arashe maganar tasa. Kuka ne ya kufce mata wanda daga ji kasan mai yinsa cike yake da fargaba da kuma tsoron halin da take ciki,ta jima tana kukan wanda su dake tsaye gurin suka kasa magana sai kallonta kawai da suke yi,ganin bata da niyyan dainawane yasa KHALEEL yin magana "Ina tunanin yanzu kam ba kuka ne abunda ya kamata kiyi ba,godiya ya kamata kiyiwa Allah da yayi sanadiyyar had'uwarmu,kafin mu wuce gida kuma" "A'aaaa!! babu inda zani........ni kam babu inda zani........bazan biku ko inaba.........kawai kuyi tafiyanku ku k'yaleni a nan.........bazan biku ba!" Ta fad'a lokacin da kukanta ya dad'a tsananta,tana ta kuka mai tsuma zuciya. HAFSAT dake tsaye har lokacin duk abunda ya faru akan idonta,duk wani furucinsu da maganganunsu ya tabbatar mata da akwai wata alak'a tsakanin wad'annan samari da *KHUBRA Y'AR GARUWA* ,cillli tayi da robber dake kanta take ta felle k'afafunta ta yanki hanya sai cikin gari,gudu take shek'awa wanda ba ita ta tsaya ba sai gaban BABA ZUWAIRA dake ta hada-hadar sallamar customer's,cike da haki take maganaa "BABA kiyi sauri ga KHUBRA can a bayan gari da wasu samari sai kuka take yi kuma" Ambaton sunan KHUBRA da tayi shi ya dakatar da ita daga abunda take yi ta mik'e tsaye cikin firgici dafe chest enta "Y'ar nan maza sanar da ni inda kika ganta tun kafin wani abu ya sameta" Cike da rud'ewa take musamman jin ance KHUBRA'N tana kuka shi ne babban tashin hankalinta saboda tunanin BABA ZUWAIRA a wannan halin samarin tareta sukayi zasu mata "FYA'DE". HAFSAT a gaba BABA ZUWAIRA a bayanta yayinda tayi k'wallo da kayan abincin ta marawa HAFSA'N baya sunata faman fakaka sauri kamar wad'anda zasu tashi sama.. Kukanta take tuk'uru yayin da ta kuma jajirce kai da fata ba inda zata bisu itakam,suna tsaka da wannan tak'addamar su BABA ZUWAIRA suka iso gurin,har kuma lokacin ta kasa yin shiru daga kukan da take yi. "Y'ar nan ina fatan kina lafiya" BABA ZUWAIRA ta fad'a tana shafa jikin KHUBRA'N dake tsaye. Da sauri KHUBRA ta k'ank'ameta tana sake sakin kuka "Ni bazan bisuba,a nan zan ci gaba da zama gurinki" Maganarta ta d'aurewa BABA ZUWAIRA kai cike da mamaki ta d'agota suna kallon juna ta kuma furta "Yi shiru ki sanar da ni,ina ne baza ki bisu ba?" "Gida zasu maida ni,ni kuma ba zan bisu ba,ni gaskiya a nan zan ci gaba da zama gurinki" Kallonsu tayi d'aya bayan d'aya,sai yanzun ta soma d'aukan haske game da lamarin nasu da kuma inda maganar KHUBRAN ta nufa,cike da jin dad'in Allah ya kawowa y'ar tata k'arshen wannan rayuwar k'uncin take fad'in "ALHAMDULILLAH!Lallai Allah shi ne abun godiya a kowane irin yanayi,Allah ya amshi rok'onmu da addu'o'inmu da muka jima munayi,Allah mun gode maka" Idanunta d'auke da k'wallar farin ciki take ta magana,kafin talli KHUBRA "Bai kamata muci gaba da tsaiwa a nanba,muje gida tukun sai muyi magana ina ganin hakan zaifi" Fuskarta d'auke da wani irin expression da ba zai fassaruba suka mik'i hanya da niyyan komawa cikin gari,inda KHALEEL yayi saurin zuba ruwa a motan ya biyo bayansu dan su kam har sunyi gaba basu tsaya jiran shiga motaba.... 《《》》 Shigowanta gidan kenan daga hospital,shima daga dukkan alamu ta dawone dan yin wasu uzurorin kafin ta koma. Wayanta ne ya shiga kuka a parlor saboda nan ta ajiye hand bag en da ta shigo da shi yanzun,tana shirin shiga kitchen kasancewar gidan babu kowa duk yaran sun tafi skul saboda yau en ta kama monday ne shi yasa take ta komai cikin sauri duk dan ta kammala kafin dawowarsu. Kukan wayan da ta jiyo shi ya fito da ita daga kitchen en cikin sauri ta d'auka dai² lokacin da kiran ya zama missed,d'an janye key en tayi sannan ta duba number da aka kiratan da shi,kafin tayi wani yunk'uri wani kiran ya sake shigowa cikin sauri ta d'auka "Assalamu alaikum!SON mutanen DUTSE ince dai ba cewa za kayi kuna hanya ba ko?" Sai da yayi wani murmushi mai cike da sauti wanda yake nuna yana tattare sa tsantsar farin ciki sannan ya amsa mata "UMMINAH barka da safiya da fatan duk kuna lafiya" "Lafiya k'alau muke SON ya mutanen gidan?" "Wallahi suna lafiya UMMI duk suna gaidaku" "Muna amsawa kun samesu lafiya dai ko?" "Ehh!to lafiya k'alau dai za ace,amma dai kam UMMI KAKA ba shi da lafiya kuma ya jima cikin ciwon,ya jikin MAMA?" "Too HAJIYA MURJA dai kam da sauk'i za ace,ammafa har yanzun tana nan kamar yadda kuka tafi kuka barta,bata san waye akanta ba ni kam wannan ciwo nata yana bani mamaki wollahi,yanzun jiran dawowarku nake muji yanda za ayi gaskiya ciwonta baya buk'atar a zuba ido hakanan,tunda nan en babu wani ci baba da ake samu" "To UMMI in sha Allah muma muna nan kan hanya nan da anjima kad'an,yanzunma akwai wani abu ne mai muhimmanci da ya tsaidamu,amma idan mun k'araso za kiji labarin koma mene ne wannan abun" Sai da tayi murmushi sannan ta ce "To SON Allah ya kawo ku lafiya kuma Allah yasa muga Alkhairi" Su duka sukayi dariya sannan ya amsa da "Ameen" yayi mata sallama akan sai sun k'araso... 《《》》 Yau tun da ta tashi jikinta yayi zafi saboda zazzafan zazzab'i data tashi da shi,kusan sati uku kenan tana fama amma ta kasa fita taje asibiti ko dan samawa kanta sauk'in ciwon dake damunta.. Shigowar babban mutumin kenan ya shiga cire kayansa kamar ko wane lokaci da hakan ya zame masa d'abi'a,da duk inda yaje ya dawo tofa yana shigowa zai hau tub'ewa kamar wani k'aramin yaro dake son mahaifiyarsa tayi masa wanka. Saman gadon ya shiga haurowa yana shafata kafin ya d'age gefen duvet en data rufu da shi,cikin jikinta ya shiga k'ok'arin shigewa,ita kuma sai dad'a matsawa baya take saboda a yanzun kam bata jin zata iya tab'uka komai a rayuwanta,sosai ya manna jikinsu da juna duk uban zafin da jikinta yayi hakan bai hana shi fara abunda ransa ke soba,cikin wahalalliyar murya ta bud'e baki iya k'arfinta "Dan Allah ka k'yaleni yau kam bana jin dad'i gaba d'ayafa kana jin yadda jikina yayi zafi ko wanka na kasa yi saboda rashin k'wari da jikina ke fama da" Duk maganarta hakan baisa ya saurara mataba,saima shinshinata da yake yana wani fiddo da harshensa kamar kare tare da sakin wani irin numfashi. "Kinsan dai a yanzu kam yadda nakai wannan matakin ba zan iya jurewaba,babu wani hak'uri da zan iya yi a halin yanzu,kawai dai kiyi hak'uri ki bani had'in kai mu ragewa juna zafi" Ko d'aya cikin maganganunsa babu ko guda d'aya wanda ta iya ganewa saboda ta kai mak'ura gurin wahala,shi kuma duk da haka bai d'aga mata k'afa ya kyaleta ba,saima dad'a k'ok'ari tare da himma da yake gurin ganin ya cimma burinshi na biyan buk'atarsa. Ba shi ya kyaletaba sai bayan da ya tabbatar da he is well satisfied,sannan ya sauka a kanta had'e da cilla mata damin kud'i "Ga shinan kije kiga likita,ni fita zanyi idan kin dawo muyi waya" Daga haka bai jira jin komai daga bakinta ba ya shige toilet en hotel en,har ya gama shirinsa ya fice MA'U na kwance ta kasa tab'uka komai kuma bata d'aga kai ta kalle shiba,da k'yar ta iya lallab'awa ta yi wanka shima jikinta sai kyarma yake haka dai ta shirya ta fice tare da kulle k'ofan ta nufi hospital... 《《》》 Lokacin da ya gama waya da UMMI yayi dai² da isowarsu k'ofar gidan,yana kallonsu suka bud'e gidan suka shiga,hakan ne yasa shi fitowa shima ya kulle motan sannan yabi bayansu. A tsakar gidan ya tarar da su suna zaune kan tamarma sunyi jigum-jigum. Guri ya samu ya zauna,sannan suka gaisa da BABA ZUWAIRA wacce KHUBRA ta kanainaye kamar wani yace zai tafi da ita duk ta hanata sukuni. "Samari duk da dai ganinku nayi sama ta ka,hakan ba zaisa nayi saurin yanke hukunci ba,nasan dai duk inda akaje aka dawo kuna da alak'a da KHUBRA kuma alak'a mai k'arfi,duba da ganin yadda kuke kama da juna" Kallon-kallo akayi tsakaninsu su uku kowa na burin gano abunda BABA ZUWAIRA ke fad'a a tare da d'an uwansa hatta da kuwa ita kanta KHUBRA dake kwance sai da ta d'ago tabi su KHALEEL da kallo. "Tabbas ku en y'an uwane na hak'ik'a ko ban tambayaba nasan ku yayunta ne" Tana magana da fara'a akan fuskarta tana kuma binsu da kallo,tun kafin BB yayi magana KHALEEL yayi tsalle ya dire da fad'in "K'warai kuwa mu yayunta ne,tun bayan b'acewarta da muka yi neman bamu sametaba wanda ya had'a da jami'an tsaro a ciki,kaf cikin gari sai da aka dubata amma ba a ganta ba,ashema tana kusa-kusa damu kawai dai Allah ya nufa hakan dai sai ya faru" Yayi shiru yana kallon BB daya kafe shi da kallo,ita kuwa KHUBRA kanta ta sauke k'asa tana sauraron maganganunsu. "To ALHANDULILLAH tunda dai yau Allah ya nunamin wani naki KHUBRA kuma in sha Allah a yau ba sai gobe ba zaki bi danginki ku koma gida,saboda dama zamanki tare da ni ba shi ne mafi a'ala ba,ki zauna tare da danginki shi ne babban kwanciyar hankali kuma kema da su duk zakufi samun nutsuwa saboda kuna tare da juna. Ni da kike tare da ni Allah ne ya had'amu kuma ina fatan Allah ya sake sadamu cikin amincinsa da alkhairinsa,yanzu zan baku labarin yadda akayi na samu KHUBRA da kuka ganmu tare" Take ta shiga labarta musu yadda akayi suka had'u da zamansu tare tun daga ranar da ta fara ganinta kawo yanzun da suke zaune suna sauraronta ba tare da ta b'oye musu koda wasali ko harafi ba. Jikinsu duk yayi sanyi kan irin wahalar da ta sha da irin rayuwar da tayi duk da kuwa sun ganta kan sana'ar tata,kallon tausayi had'e da al'ajabin yadda ta juri wahalar sana'ar suke binta da shi kafin daga bisani suka sako maganar tafiya da KHUBRA'N. Haka BABA ZUWAIRA ta shiga d'aki ta had'a kayan duk data san na KHUBRA'N ne ta fito,tana d'an matse idonta da k'walla ta tarun mata. Mik'ewa sukayi cikin shirin barin gidan,nanfa KHUBRA da BABA ZUWAIRA da suka ga dai tabbas tafiyar nan zasu yi,suka k'ank'ame juna suna kukan rabuwa da juna a lokacin da d'ayansu bai tab'a tsammanin faruwar hakanba. KHALEEL ne ya ja BB gefe yana fad'in "MAN baka jiba" 'Dan matsawa BB yayi jikin KHALEEL tare da kallonsa yana d'aga masa kai "Gaskiya a shawarana ina ganin rabasu yanzun akwai damuwa duba da yadda suka shak'u da juna,ina ganin me zai hana mu tafi da su duka kaga ta wani b'angarenma BABA'N zata mana amfanifa ko kuwa me kake gani?" Shiru BB yayi yana hasashen maganar KHALEEL en sannan kuma ya d'an daki kafad'ansa "Yeahhh!ka kawo shawara mai kyau kawai muyi hakan" Komawa gurin da su KHUBRA suke tsaye sukayi har lokacin suna manne da juna,KHALEEL yana y'ar dariya yace "Ina ganin BABA da kun daina kukan nan haka nan,saboda mun yanke shawaran tafiya dakune duka" Da sauri KHUBRA ta d'ago kanta ta kalleshi,shi kuma ya kad'a mata kai dan ya fuskanci so take ta tabbatar da abunda ya fad'a. Aiko da sauri ta shiga gogewa BABA ZUWAIRA hawayenta itama ta goge nata tana dariya,cikin sauri ta shiga d'akin ta d'ebowa BABA ZUWAIRA kaya sannan suka d'unguma suka fice daga gidan,sai da ta shiga mak'otanta tayi musu sallama,tukun ta dawo inda ta barsu a k'ofar gidan jikin mota,daga nan suka shige tare da d'aukan hanya sai cikin gari wato cikin k'waryar KANON DABO....................... *~#TEAM KHUBRA.~* *_#REAL SMASHER._* 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *4/ʝųlყ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *4⃣0⃣* *"B* EAUTY me ya sameki kike kuka?wani abu yana damunki ne?" BIGGY ne yake wannan maganar cikin rud'ewa yana tambayar ASHNA dake sunkuye ta had'a kai da guiwa sai risgar kuka take kamar wacce aka aiko mata da sak'on MAMA ta rasu. Kukan da take yine ta kuma k'i bashi amsa yasa ya ajiye package en hannunsa,kusa da k'afafunta ya nemi guri ya zauna had'e da lank'washe k'afafunsa,fuskarsa cikin wani irin yanayi yake kallonta "Please BEAUTY kiyi shiru hakanan ki daina wannan kukan kinji,yanzun fad'amin duk abunda kike so ayi kinji?" Da sauri ta d'ago fuskarta da tayi kacha-kacha da hawaye tana kallonsa,kai ya d'aga mata alamar da gaske yake. "Da gaske nake miki BEAUTY amma sai kin daina kukan nanfa kinji?" Da sauri ta shiga goge fuskarta ta sake kallonsa had'e da d'anyin murmushi,aifa BIGGY wannan murmushin da ASHNA tayi masa ba k'aramin tafiya yayi da shiba take kuwa ya kafeta da idanu har bai sanma tana magana ba sai da tayi clapping a dai² fuskansa,sannan yayi saurin dawowa hayyacinsa yana fad'in "Ammmm!BEAUTY me kika cene?" Da d'an mamaki ta kalleshi wato dukma maganar da tayi bai san tana yiba kenan ko mene yake nufi? Daurewa tayi ta fara magana cike da shagwab'a kamar tana gaban MAMA. "Ni gurin MAMANA nake son zuwa.....Dan Allah ka maidani gida...Ina son na san halinda MAMATA take ciki...Please kaji" Yanayin yanda take magana duk ta wani narke ita a dole y'ar lelen MAMA. Ga BIGGY kuwa wani yanayi yake tsintan kansa aciki duk lokacin da tayi magana to shi kuma nan zaiyi da nasa kan dan duk inda ta lank'wasa kanta yana biye da nasa kan,yana faman zuba murmushi. Tsuke fuska ASHNA tayi tana kallonsa da mugun haushi d'auke cikin idanunta kan yadda taga duk ya wani kafeta da ido. "MALAM lafiya kake min irin wannan kallon? Nifa kaga banson irin wannan kallon k'urillan haka kawai duk ka gano munin mutum,to gaskiya ya isheka haka" Cike da tsiwa take maganar tana zabga masa wata uwar harara,dariya yayi mata wanda yasa farare tas en hak'oransa suka bayyana,dariyan da yayi shi ya bawa beauty point dake gefen kumatunsa lotsawa,take kuwa ASHNA ta saki baki tana kallon ikon Allah "Ammafa GUY en ba laifi,duk da kasancewarsa bak'i,da wad'annan jajayen idanun nasa amma ai yana da hanci ga beauty point,wow inama ba cikin mugayen nan yake ba,kuma kyau ace yayi boko,omg ya zai kasance?" Kanta ta d'an d'age tana son tuna ya wannan GUY en zai kasance,sai dai tayi murmushi had'e da fad'in "Kaiiiii ammafa wollahi da ba k'aramin HANDSOME za ayiba" Gintse fuska ta dad'a yi ganin yadda yake sake kallonta "MALAM nafa ce maka ka denamin irin wannan kallon ko? har da wani yimin murmushi,ka rik'e abunka bance maka ina soba ai Yanzu kawai ka fad'amin zaka mai dani gidanmu?" "A'a BEAUTY bazan iya mai daki ba yanzu" "Da Allah ni ka dena wani cemin BEAUTY tunda ba maidani za kayiba,kawai ka tashi ka bani guri" Ko rufe bakinta bata yiba taga ya mik'e yana shirin barin d'akin,baki ta dad'a b'arewa tasa masa kuka. Daf da bakin k'ofan ya tsaya had'e da rufe idanunsa lokacin da take kukan,da sauri kuma ya fice daga d'akin tare da rufe d'akin... Fitowansa daga d'akin ya tsaya nan cikin corridor en,number HAJIYA LAURA ya shiga kira,bayan ta d'auka ya shiga labarta mata abunda suka yi ASHNA yanzun. Ko gama rufe bakinsa baiba HAJIYA LAURA cikin tsawa ta dakatar da shi "Nooo!BIGGY kadama ka kuskura ka tafka wannan d'anyen aikin,taya zaka biyewa wannan y'ar mitsitsiyar yarinyar Baka gudun abunda zai je ya dawo ne hala idan ka maidata gida? Ko kuwa baka tunanin gane fuskarka da tayi zai jawo mu fad'a hannun hukuma to gaskiya tun wurima ka kama kanka da wannan maganar Sam hakan ba mai yiwuwa bane ina fatan ka gane" Jiki a sanyaye yayi mata sallama ya kashe,nanfa BIGGY ya jingina jikin ginin gurin ya rufe idanunsa yana tuna irin yadda yarinyar ke nuna damuwarta da son ta koma gida ko don sanin halin da mahaifiyarta ke ciki. Tambayoyi ya shiga yima kansa "Shin mema yasa muke irin wannan aikin ga wasu mutanen da babu tausayi a zuk'atansu?ko don na rasa iyayena ne tun ina yaro shi yasa na biyewa irin wad'an nan mutanen suna sani aiki irin wannan,shin bana gudun ranar da Allah zai tashi kamani? Dame zanje masa wanda zan kare kaina a gurinsa? Gaskiya ya kamata na nutsu.....Ina buk'atar shawara daga gurin wani......Ina buk'atar canja halayena.....To amma wa zan tunkara da wannan maganar? Shi kad'ai yana ta magana da zuciyarsa,rashin samun maka yasa shi saita kansa sannan ya bar gurin jikinsa duk yayi sanyi saboda tunanin da yayi. 《《》》 Shigowar dattijon gidan kenan da sallama sai dai babu kowa tsakar gidan,hakan ne yasa shi tunkaran d'akinsa ya sanya d'an k'aramin key en ya murza tare da bud'e k'ofar yana mai kunna kai cikin d'aki. Kan y'ar lank'wamammiyar katifan ya kwanta duk abun duniya ya dame shi,zuciyarsa duk babu dad'i haka yake jinta,haka dai ya juya ya kwanta cike da damuwa da ya rasa ta mene ne. Lek'e ta shiga yi ta saman dangar karan dake kewaye da gidan duk burinta bai wuce ta hango cikin gidanba,k'ofar d'akin MALAM en ta hango a bud'e da alama ya dawo kenan. A hankali cikin sand'a ta shigo gidan,wuf tayi ta shige d'akinta da ganin yadda take tafiya kasan babu gaskiya wai akace "awo a d'aka". Wuf tayi ta afka cikin d'aki tana dafe k'irjinta had'e da fad'in "Waii Allah ya taimakeni MALAM bai kamani ina wannan sand'arba da yau kam ina da tabbacin komai zai iya faruwa" Wata irin dariya ta tsinkayo a bayanta data sata saurin juyowa tana bin inda taji dariyan da kallo Zaune saman gadonta na k'arfe ta hangoshi ya hard'e k'afafu kamar a fada Tsoro ne ya cika mata zuciya,duk da tasan waye hakan bai rage mata tsoron da take cikiba. Da k'yar take had'iyan yahu dan ta san ko me ya kawoshi a wannan lokacin,haka LADIYO ta shiga jan jiki har ta k'arasa gurinsa dan ta san bata isa ta bijireba,ko dan tsoron da take ciki,hakan ba maganin komai zai mataba. A dai² lokacin da LADIYO suke tsaka da shek'e ayarsu da HATSABIBIN BOKA'N nasu ne shi kuma ABBA'N KHUBRA yake bacci mai cike da mafarkai da ya saba yinsu ko wane dare. Cikin duhun dare cikin wani irin k'ungurmin daji da babu komai cikinsa face koke-koken tsun-tsaye da wasu halittun marasa dad'in ji. Kamar daga sama ya tsinkayo muryar yarinyar tana kuka "ABBA ka taimakeni....Wayyoo Allah ABBA zasu kashe ni....ABBA kada ka bari su cutar dani dan Allah" Abunda ya iya jiyowa kenan shima cikin wani irin sauti da yake nuna ta gama galabaita ne take masa magana. Yunk'uri yayi domin ya taimaka mata sai dai me ya kasa ko da taku d'aya saboda yadda yake d'aure jikin wani k'aton dutse,hannu da k'afafunsa duk suna sanye cikin ank'wa,wacce baya tunanin zai iya tsira daga gareta. Hankalinsa a tashe saboda ganin yarinyar da yayi wasu irin mutane da baya iya hango fuskokinsu bare yasan su waye,sun rik'eta suna tunkarar wani k'aton rami da wuta ke ci a ciki da nufin jefata,ita kuma sai turjewa take tana waigowa tana kiransa kan neman taimako daga gare shi. 'Dagata sukayi da niyyan jefata,kafin su ida nufinsu suka fara jiyo gudu had'e da haniniyar dawaki,samari ne su biyu sun ratso ta cikin jejin haye bisa dawakai fuskokinsu rufe da k'yalle,iya k'arfinsu suka bud'e baki suna furta "Laa-ilaha'illa anta subhanaka inniiy kuntu minaz-zalimiiyn" Fad'ar wannan kalmar babu b'ata lokaci yarinyar da ake k'ok'arin jefawa wuta,ta shiga maimaitawa cikin k'arfin hali da bud'e murya iyakar iyawarta. Wutar dake ci cikin ramin tayi wani irin tasowa kamar an hurota,harshen wutan da yayiwo wajensu take ya laso su wutan ta kama jikinsu suka kama da wuta,sakinta suka yi a k'asa,sai dai abun mamaki wutan ko kad'an ita bai sametaba. Cikin sauri d'aya daga cikin mahayan ya sauko tare da d'aukanta ya aza saman dokinsa ya haye shima. Da gudu suka bar jejin inda take a nan shi kuma ya dena ganinsu sun b'ace b'at kamar iska. B'acewan nasu ya dad'a jefa zuciyarsa cikin tsananin tsoro da fargaba,kamar daga sama yaji yo muryan yarinyar lokacin da take maimaita abunda taji wad'annan mahayan sun ambata. Yunk'urin fad'a ya shiga yi shima,inda yana maimaitawa yaji ank'wan dake d'aure jikinsa ta zube k'asa,juyawa yayi ya kalli jejin gaba da baya sannan ya shiga shek'a gudu iya k'arfinsa ta hanyar da yaga sunbi,yana cikin gudun ya fara hangosu can nesa da shi,sosai yake gudun kamar wanda ya hau takalmin taya sai da ya kusa cimma mahayan duk da kasancewar suna kan abin hawa shi kuma yana k'asa,har ya fara murna kawai sai ji yayi ya daki wani irin dutse a gabansa da ya sashi fad'uwa a gurin,kansa ne ya daku da dutsen take idanunsa suka soma k'ank'ancewa saboda azaba... A firgice ya farka jikinsa duk ya had'a zufa duk kuwa da yanda garin yake cike da iska saboda hadirin daya had'u a d'azun sai dai iska kawai ya bayar mai sanyin dad'i,amma shi gare shi duk ya jik'e da gumi. Tunanin mafarkin da yayi ya tsaya yi,yana mamaki had'e da al'ajabin mene ne had'inshi da mafarkin? K'wak'walwarsa ta dawo masa da maganganun yarinyar da yayi mafarki da ita,take ya tsinci kansa da fad'in "Laa-ilaha'illa anta subhanaka inniiy kuntu minaz-zalimiiyn" Maimaitawa yayi tayi cikin zuciyarsa,wanda k'arshe har kalmomin suka bayyana a fili. Jiki a sanyaye ya mik'e daga gurin yayi hanyan fita daga d'akin zuciyarsa wasai babu zafi da kuma rad'ad'in da yake ji a baya. Har ya d'auki buta zai shiga bayan gida ya dawo tare da ajiyewa a gefen randa,k'ofar d'akin LADIYO ya tunkara,kasancewar yasan su kad'ai ne a gidan ba tare da ya k'wank'wasaba ya kunna kai ciki da y'ar torchlight ensa da yake haska hanya da ita. Mugun gamon da yayi yasa shi dafa bango saboda wani jiri da yake neman d'ibansa,cikin sauri kuma ya juya ya fice daga d'akin zuciyarsa na k'una....... Tashin hankali kenan wanda ba a sa masa rana... 《《》》 Misalin k'arfe 1:40pm motan ta kunno kai cikin haraban gidan,har lokacin KHUBRA na lafe jikin BABA ZUWAIRA,baiwar Allah tana zaune sai kalle-kallen cikin gari take,har suka k'araso cikin gidin wanda had'uwa da tsarin gidan yasa take bin ko'ina da mamakin yadda akayi KHUBRA ta iya rayuwa a wannan k'ungurmin k'auyen nasu kuma har ta iya jurar wannan wahalar. KHALEEL dake driven yayi parking sannan ya fita,inda BB shima ya mara masa baya yana fitowa ya ja k'ofan baya inda su KHUBRA suke,cikin taushin murya ya furta "Bismillah" Had'e kuma da nuna musu hanya suka fito KHUBRA rik'e da hannun BABA ZUWAIRA suka bi bayansa,KHALEEL a gaba BB biye da shi sai kuma su KHUBRA dake bi masa. Ummi tsaye cikin kitchen tana gyara zaman warmer's en akan tire da take son fita dashi,gefe kuma basket ne shima da wasu had'ad'd'un Flak's,tana shirin fitowa sallaman su ta kawo kunnenta. Da sauri ta fita tana fad'in "Lale marhaban da Y'AY'ANA,gaskiyafa kunsha hanya" Turus ta tsaya tana kallonsu ganin ba su kad'ai suke tafeba.. "A'aa da bak'i kuke tafe ashe,amma ya akayi baka sanar da niba da kayimin waya?" Ta kalli KHALEEL cike da tuhuma,kunnensa ya d'an rik'e alaman ban hak'uri,murmushi tayi tare da fad'in "Ai kaikam ka iya bada hak'uri idan kayiwa mutum laifi" Kallon BB tayi da ya riga ya zauna tana k'arasawa dinning lokacin da ta ajiye tiren hannunta, sannan ta dawo cikin parlor "Sannu SON kun sha hanya" "Wallahi kuwa UMMI mun sha hanya,amma ai duk ga wanda ya jaa muka kawo yanzu bamu isoba,ya wani tsaya drive'n kamar d'an koyo" "Oooo!nikam naga ranar da zaka fara drive'n a hankali,wato kaii dai kawai kafi son ayita shek'a gudu ko?" "Yawwa UMMI ai haka shi ne magana" "Uhmm Allah ya kyauta muku" "Ameen UMMI'NMU" Ya fad'a yana sakin murmushinsa mai kyau.. "Ooooo!kunga kun sani surutu daga zuwanku ko bak'in ban bawa gurin zama ba" UMMI ta fad'a tana nufan inda su KHUBRA ke tsaye har lokacin sun kasa samun gurin zama. "Bismillah mana kuna tsaye har yanzu" Ta fad'a tana nuna musu sofa,k'in zama sukayi suka nemi guri nan k'asa kan rug BABA ZUWAIRA tana fad'in "Nanma ya isa wallahi" "Yawwa UMMI kin gane su kuwa?" KHALEEL ya katseta lokacin tana shirin yin magana "Yau kam kujimin yaro ta ina zan ganesu tunda ba bayani kuka yiminba" Dariya ya tsaya yi yana fad'in "Shi kenan UMMI tunda dai baki ganeba,amma bari ZUHRA ta dawo muga" Shiru tayi tana kallon mutanen,haka dai suka gaisa ba tare da ta shaida mutanenba kuma bata tambayaba,kiran sallah ne ya katsesu daga maganar da suke yi kan haka ne suka tashi su kuma suka fice zuwa MASJEED ba tare da sunyi mata bayaniba. _ AFTER FEW MINUTE'S._ ZUHRA ce a gaba sauran yaran na biye da ita bayan fitowansu daga mota lokacin da driver ya saukesu suka nufi hanyan parlor. Da sallama suka shiga saboda hakan duk yana cikin irin warning da BB yayi musu kafin zuwansu gidan,kuma har ranar babu wanda yayi kuskuren aikata wani laifi,shi yasama duk abunda ZUHRA tayi to suma zaka samesu masu aikata hakan saboda gudun had'uwansu da shi. KHUBRA dake zaune lokacin ta idar da sallah tana jiran BABA ZUWAIRA ta idar da salla'n ta jiyo sallama'nsu,amsawa tayi mai sallama ta shigo sannan yaran dake bayanta suka shigo suma,idanunta ne suka sauka kan KHUBRA dake zaune saman rug ai tuni cikin abunda baifi second's ba tayi cilli da jakan hannunta ta kwala wani k'ara lokacin ne kuma ta saki kuka dai² tana k'ank'ame da KHUBRA'N. Kuka su duka biyun suke yi sun rik'e juna,dai² nan su BB suka shigo,tsayawa kallon ikon Allah sukayi kafin suka kalli juna suna kuma d'agawa juna kai da alaman tambaya a fuskokinsu Dariya sukayi ganin yadda sukayi a lokaci guda,sannan suka k'arasa cikin parlor'n...... 《《》》 Cikin hospital en ta shiga bayan ta amshi card,sannan ta jira layin ganin likita,lokacin da aka zo kanta bayan ta shiga gurin likitan,yayi mata tambayoyi tana bashi amsa. Kallonta yayi sannan ya maida hankalinsa kan card en yayi y'an rubuce-rubucensa. Bayan wasu y'an mintuna ya d'ago yana kallonta fuskarsa cike da wasu irin alamu. Hankalin MA'U duk ya gama tashi tana kallonsa dan bata san mene ne zai fad'a ba a halin da ake ciki. Cike da zak'uwa na son tasan me yake faruwa dan a lokacin kam har ta nemi ciwon ta rasa na wucin gadi "Dan Allah likita ka sanar da ni abunda yake faruwa,wallahi duk na kasa samun nutsuwa saboda fargaban ban san me zaka ce yana damuna ba" Dogon numfashi ya sauke sannan ya fara magana "Ehhh!to bisa ga yadda dai kika yimin bayani,akwai abunda nake zargi game da ke,sai dai bazan tabbatar mikiba har sai kinje laboratory anyi miki gwajin jini" Dumm!taji gabanta ya fad'i kanta ta sunkuyar k'asa,kome ta tuna kuma tayi dabaran saita kanta,sannan ta karb'i y'ar takardar dake hannunsa ta fita. Da tambaya ta samu ta isa gurin gwajin jinin,bayan y'an mintuna data jira aka bata sakamako ta sake kamo hanyan office en likitan,tana tafe zuciyanta na tsinkewa haka har ta k'araso. Knocking tayi daga ciki aka bata izinin shiga ta ko danna kai ciki,zaune yana ta rubuce-rubuce kan wasu file's. Shigowanta yasa shi tattara wasu daga ciki daya gama amfani dasu ya nufi gurin wani vault ya zura,sannan ya dawo ya zauna had'e da amsan sakamakon nata. Envelope en ya bud'e ya janyo takardar dake ciki ya shiga warwarewa,duk abunda yake yi idanun MA'U na kai tana sauraren jin me zai biyo baya. Idonsa ya d'ago ya kalleta sannan ya sake yin rubutu saman card enta. Muryarsa ta tsinkayo yana fad'in "A sakamakon bincike da ya faru bayan hasashen da nayi hakan ya tabbatar mana da kina d'auke da....................... _~Ina so nayi amfani da wannan damar gurin sanar daku fan's ba lallaine nan da kwanaki 3 kuga posting enaba saboda bikin friend ena da zamu fara,amma idan na samu sararin yin typing zaku jini in sha Allah, na gode.~_ *~#TEAM KHUBRA.~* *_#REAL SMASHER._* 💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *10/ʝųlყ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* _Masoya ina baku hak'urin jina da kukayi shiru kwana biyu duk da dai na sanar daku dalilin faruwar hakan,amma ku k'ara hak'uri akan na da da kukayi..Na gode._ *~___________________________~* _Wanna page en tukuici ne gareki y'ar uwata kuma k'awata,ina miki fatan alkhairi a duk inda kike na tayaki murna mara misaltuwa da wannan rana mai tarin alkhairi wacce tazo da sauyi a rayuwarki baki d'aya,ina addu'a tare da fatan wannan farin ciki ya ci gaba da tabbatuwa tare dake har k'arshen rayuwarki,ina miki murnan ganin rana mai cike da d'umbin tarihi rana da ta kasance ta aurenki tare da angonki,ina muku fatan dawwama cikin wannan farin ciki._ *SADIYA ISHAQ ISAH* _DA_ *MUHAMMAD BILAL SHEHU* _Allah ya baku zaman lafiya tare da hak'uri da juna.Allah kumavya kawo na y'an baya.Ameen thumma ameen._ *~___________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *4⃣1⃣* *C* ikin parlor suka shigo kowanne ya nemi guri ya zauna suna jiran UMMI ta iso dan suyi mata bayanin abunda ke faruwa kan bak'in da suka zo da su. Suna zaune suna kallon KHUBRA da ZUHRA da har lokacin sun gagara yin shiru,sai faman risgar kuka suke kamar wad'anda akawa mutuwa. Babu wanda yayi musu magana kan kukan da suke,har sai da sukayi ya ishesu sannan kuma suka shiga kallon juna suna murmushi,lokaci d'aya suka kai hannayensu kan fuskokin juna suna goge hawayen dake fuskokin nasu,duk abunda suke yi BABA ZUWAIRA,BB,KHALEEL dama sauran yaran dake parlor'n akan idanunsu hakan ke faruwa illa UMMI kad'ai da bata nan. "Wai YAYA ZUHRA wace wannan en da kuketa kuka ke da ita kuma me aka muku?" FATAHIYYA tayi tambayar tana yamutsa fuskarta. Sai da ZUHRA tayi murmushi sannan ta kalleta tace "Baki ganeta ba ko?" "To kema dai YAYA ZUHRA ta yayama zan santa,ni da ko ganinta ban tab'a yiba" 'Dan murmushi ZUHRA ta sake yi hannunta sak'ale cikin na KHUBRA sunata yiwa juna murmushi "Uhmmmm!ba abun mamaki bane dan kince baki santaba ai To ba wata bace wannan en face KHUBRA" Mik'ewa FATAHIYYA tayi hannunta dafe da k'irjinta tana nuna KHUBRA'N,ko kafin ta kaiga yin magana UMMI ta fito tana maimaita sunan KHUBRA'N itama "Yanzu dama doughter ke ce kika koma haka?har na kasa ganeki haka?" Tana kallonta wanda babu komai cikinsa sai zallan tausayi da kuma ganin yadda ta koma cikin k'ank'anin lokaci duk ta yamutse kamar ba itaba. Kusa dasu UMMI ta dawo ta kama KHUBRA'N tana kallo mamaki fal a tare da ita "Ko tantama babu wannan KHUBRA ce,ku kuwa yaran nan a ina kuka samo mana ita?" Parlor'n yayi shiru babu wanda yayi yunk'urin yiwa UMMI magana bare har tasa ran samun amsa daga bakinsu. Ita ko BABA ZUWAIRA mamakinta baya wuce yadda KHUBRA'N take da y'an uwa masu sonta haka amma har ta daure tayi rayuwa tare da ita a cikin wannan k'ungurmin k'auyen,sai binsu da kallo take na sha'awa tana d'an murmushi. "Wai SON a ina kuka ganota ne?" UMMI ta sake yin tambayan a karo na biyu. Sai da ya sauke dogon ajiyan zuciya kafin BB en ya d'ago daga danna wayan da yake yi. Filla-filla ya warware mata yadda suka had'u da labarin da suka tsinta na irin rayuwar da tayi a k'auyen na ZAKIRAI har zuwa tahowarsu dasu ba tare da ya rage ko da wasaliba a maganarsa. ZUHRA dake da rauni tun ana bada labarin take kuka kowa yana iya jin sautin kukanta a fili,yayin da ta dad'a k'ank'ame KHUBRA wacce ta sunkuyar da kanta k'asa tana saurarensu. UMMI kam dauriya kad'ai tayi batayi kukanba amma kam zuciyarta ta gama karyewa,godiya take ta yiwa Allah da KHUBRA'N bata sanar da matar komai game da halin da take cikiba kafin b'acewar tata da asalinta ta barta akan su en family enta ne,lallai kuwa suma zasu nuna hakan har zuwa matar ta koma inda ta fito. Jikin FATAHIYYA yayi sanyi sai kallon KHUBRA take tana goge siraran layin hawayen dake fuskarta,yau kam ta d'auki darasi cikin rayuwar KHUBRA da suka sakama k'ahon zuk'a kan ganin bayanta,a dai² lokacin ne kuma ASHNA ta fad'o mata,aifa nan ta shiga kuka sosai saboda da farko kukan nata ba mai sauti bane amma tuna y'ar uwarta ta jini da aka sace a kan idanunsu ya dad'a tada mata hankali wanda yasa lokaci guda sautin kukanta ya fito fili. Babu wanda yayi yunk'urin hanata a cikin parlor'n saboda kowa da abunda yake ji a zuciyarsa. *SOME MINUTE'S LEPT* Bayan zaman alhini da sukayi na y'an mintuna sannan kuma suka soma shirin tafiya hospital,duk wani motsi da KHUBRA za tayi ZUHRA na biye da ita tamkar chewing gum haka ta zame mata,ita kam sai dai tayi murmushi idan ta kalli ZUHRA,su kansu sauran jama'an dake gidan suna mamakin wannan soyayya da shak'uwa idan aka cire BABA ZUWAIRA da bata san ainihin *GASKIYAR LAMARI'N* ba. *AFTER 2 DAY'S* Kimanin kwanaki biyu kenan da bayyanar KHUBRA wanda ko kad'an UMMI bata barinta ta bisu hospital duk kuwa da tsananin nacin da take yi kan bin nasu,sai yau da taga KHUBRA'N ta d'an soma washewa daga wannan azababben duhun da tayi na daud'a data manne mata a jikinta. Haka suka kammala shiri bayan UMMI tasa KHUBRA sake yin wanka da sabulai masu kyau da k'amshi,sannan tun daga zuwanta gidan UMMI tasa ta cire tsummokaran dake jikinta wanda suka sauya mata halitta tamkar *Y'AR ALMAJIRA* bayan nan kuma suka d'unguma zuwa hospital... 《《》》 BIGGY zaune a parlor yanata tunanin maganar BEAUTY'NSA da har yau bai san takaimaman sunantaba,yau kimanin kwanaki sati guda kenan da tayi masa maganar tana son ya taimaketa ya maidata gida,kuma tun daga ranan ne bai sake komawa d'akinba sai dai ya aika a kai mata abinci. Tunanin hanyar da zaibi ya magance duk wata damuwa dake neman kunno masa kai yake,yana nan yana tunani kiran HAJIYA LAURA ya shigo wayansa,kallon saman screen en yake ya k'ureshi da ido kamar mai son gano wani abu a jikin sunan dake lilo saman wayan,har kiran ya katse ba tare da yayi yunk'urin d'auka ba. Yana kallo wani kiran ya sake shigowa wayan amma baiyi yunk'urin d'aukaba,haka tayi ta kira har ta gaji ta kyaleshi. Tun safe yake gurin a zaune ba tare da yayi yunk'urin yin komaiba har misalin k'arfe 4:00pm sallah kad'ai ke fad'a shi a zaman gurin saboda duk iskancin BIGGY baya tab'a yadda sallah ta wuceshi,kamar wanda aka tsikara ya mike yana nufan hanyan bedroom en da take ciki. Zaune take kamar kowane lokaci ta had'a kai da guiwa tana ta jan zuciya saboda kukan da ta jima tana yi. Zama yayi a gabanta wanda yasa tayi saurin d'ago jajayen idanunta ta kalleshi tana jiran jin dame yazo yau kuma. Kallon yanayinsa tayi duk ya wani koma silent da shi,kanta ta sunkuyar tana sauraron jin me zai ce. Har kusan mintuna biyar ya d'iba yana zaune yayi shiru ba tare da ya iya furta komaiba,sannan yayi ajiyan zuciya cikin sanyin murya dake nuni da mai maganar yana tare da wani yanayi na damuwa a hankali ya furta "BEAUTY dan Allah kiyi hak'uri da abunda ya faru,tun daga ranar da muka d'aukoki har zuwa yau da nake zaune a kusa dake ina son ki yafemin,tabbas shigowarki rayuwata ya sauyamin tsarina kuma ya canja ni gaba d'ayana,tun daga lokacin dana rasa mahaifana ban sake tunanin zan koma mutumin dake da tausayi a zuciyarsa ba ko dai² da d'igo d'aya amma zuwanki yana neman mai dani wani a rayuwa,zuwanki ya kawo haske cikin rayuwata,nayi alfahari da hakan ta faru,amma ina so kiyi hak'uri da abunda mukayi miki sannan". Yayi shiru na d'an wani lokaci yana nazarin me zai fad'a kuma wanda zaisa tayi magana Kallonsa kad'ai ta tsaya yi tana mamakin kalmomin da suke fitowa daga bakinsa,tausayinsa ne ya bijiro mata jin shi d'in marayane,wasu siraran hawaye ta goge tana d'aga masa kai ba tare da tayi magaba. "In sha Allah daga yau babu wanda zai sake sani aikata irin wannan d'anyen aikin,rashin iyaye ba hauka bane da har wani zai dinga juyamin tunani ta har sani aikata ayyukan marasa imani".. 'Dan murmushi ASHNA ta sake yi tana sauraron maganarsa dake tafiya kai tsaye cikin zuciyarta Tashi yayi da niyyan barin d'akin,wanda ASHNA sam bata san me yake afkuwa ba,saboda yadda take ta tunanin abubuwa da dama akansa,dai² bakin k'ofa ya dakata sannan cikin sanyi yace "Ammm!ina ganin yanzun ya kamata kiyi shirin komawa gida,yanzun in Allah ya yarda zan maida ke" Yana kaiwa nan a maganarsa yayi waje da sauri dan bata damar shiryawa. Dariya game da hawayen farin ciki suka had'e mata lokaci guda,farin cikinta a wannan lokacin baya misaltuwa,cikin gaggawa ta kimtsa sannan ta fito daga d'akin rana ta farko tun bayan shiganta d'akin kenan da ta fito a hankali take bin corridor en tana wucewa har ta iso dai² stair's,sakkowa take jikinta yayi mata sanyi duk da tafi damuwa da son komawa gida,a parlor ta tarar da shi yana zaune ya d'ora hab'arsa a kan hannayensa da alama tunani yake,sai dai kuma sakkowanta yasa shi binta da kallo had'e da k'irk'irar murmushi,hakan ya tabbatar da baiyi nisa a tunaninba kenan.Mik'ewa yayi ita kuma tana binsa a baya har suka isa parking space na gidan,sai yanzun ta samu daman kallon gidan,babbane sosai ko dan da dare ne wancan ranan shi yasa bata iya tantancewaba. A hankali ta d'age kafad'anta tana fad'in "Ohooo ina ruwana a ciki wai kam???" Kafin ta sake yunk'urin yin wani tunani har ya bud'e motan tare da mata nuni data shiga,babu musu ko ta shige shi kuma ya zagaya d'ayan side en ya zauna sannan yayi starting motan,cikin k'ank'anin lokaci suka fice daga gidan suka hau hanyan da zata sadasu da RIJIYAR ZAKI... 《《》》 Shirun da DR en yayi ne ya dad'a tada mata hankali to kuma me yake son sanar da ita haka,bakinta har rawa yake yi wajen son tambayarsa abunda ya gani a jikin result en nata. "Dan Allah likita ka sanar dani abunda yake faruwa da har yasa kayi shiru kak'i sanarmin" Wani ajiyan zuciya ya sauke sannan ya sake kallonta. "No hajiya ba wani abu ke damunkiba kawai dai zazzab'i ne maybe kuma akwai abunda bakya amfani da shi da kika soma using nasa cikin y'an kwanakin nan,so ina ganin babu wata matsala,yanzun zan d'oraki kan magunguna idan yaso nan da wani lokaci idan bakiji sauk'iba sai ki dawo don a chanja miki da wasu" Wani wawan ajiyan zuciya ta sauke sannan a hankali ta iya furta "Ai ni wallahima DR har ka bani tsoro da kalamanka na farko kwata-kwata banyi tsammanin wannan ne abunda zai fito daga bakinkaba" A kaikaice ya kalleta saboda rashin amincewa da maganar tata,shi kam baisan dalili ba da yasa yake mata wani irin kallo,saurin yin rubutu yayi ya mika mata card en sannan ya furta "Hajiya ai babu abun tada hankali anan saboda jininki ya nuna 'NEGATIVE' da ya koma 'POSITIVE' ne zamu iya cewa akwai matsala" Duk bayanin da yake mata ba wani gane negative da positive da tayi saboda bata san me hakan ke nufiba,murmushi tayi kawai ta amsa card en tana masa godiya sannan ta fice.. Bayan fitanta ya tsaya yana bin k'ofan da kallo,haka kad'ai yake tunani wannan matar da gani kaga irin y'an duniyan nan,kome ya tuna kuma yayi saurin kawar da tunanin ta hanyar janyo ragowar file's dake kan table en ya shiga bud'ewa yana ci gaba da aikinsa.... 《《》》 Sallah yaketa jerowa babu sassautawa tun yanayi yana iya gane abunda yake karantawa har ya zamana idanunsa sun koma sai haske kad'ai yake gani cikinsu babu wani abu da yake iya shaidawa cikin d'akin bare har ya iya nuna muhallinsa,zaman tahiya yayi sannan ya sallame,zuciyarza tayi k'uncin da baya iya bambance tsakanin fari da bak'i. Zama yayi had'e da tank'washe kafarsa cikin yanayi dake nuni da yana tattare da matsananciyar damuwa da bata da iyaka a wannan lokacin. Yarinyarsa ce ta fad'o masa tunaninta duk ya addabeshi,take ya goge fuskarsa ya fito daga d'akin,d'an k'aramin d'akin da yayi bak'i wanda ke nuni da d'akin girki ne ya nufa da niyyan tasota tayi sallah a tunaninsa tana ciki kawai dai sha'afa yayi bai tasheta ba hakan yasa yake ta sauri dan yadda shima yake ganin yau d'in ya makara. Babu komai cikin d'akin face tarkacen kwanukan girki,tsayawa yayi turus yana bin gurin da kallo,wani irin tunani ya soma yi wanda a k'arshensa babu komai sai tsananin firgici da yasa ABBAN KHUBRA sake nufar d'akin LADIYO kamar zai tashi sama dan sauri... 《《》》 Tun shigansu d'akin da MAMA ke kwance kamar gawa bakinta da hancinya sakaye cikin abun daidaita numfashi,kowa jikinsa ya dad'a sanyaya kamar an jefi kaza da gishiri. Kusa da gadon MAMA KHUBRA ta matsa saboda tun shigowarsu hankalinta na kanta abun tausayi haka ta zauna gefenta hannunta ta rik'o had'e da damk'ewa cikin nata,nan da nan hawaye suka soma sakkowa daga idanunta,sheshek'an kukanta kad'ai suka tsinkayo BB,UMMI,KHALEEL dama su kansu sauran da suke cikin d'akin,sai dai abunda tayi ya basu matuk'ar mamaki dan suna da tabbacin irin k'iyayan da MAMA kewa KHUBRA. Cikin muryar kuka take tambayan ZUHRA "Me ya samu MAMA'N haka?" Cikin ALHINI ta bata amsan duk abunda ya faru sannan kuma da dalilin kwanciyan MAMA'N jinya. Bakinta ta shiga motsawa tana mata addu'a wacce ANNABI (S.A.W) ya koyar damu a duk lokacin da wani yake halin jinya wato _(AS-ALULLAHAL AZIIYM RABBAL ARSHIL AZIIYM AN-YASHFIYAKII ×7)_ Sannan ta sake k'arawa da _(LAA BA'ASA 'DAHURUN IN-SHA-ALLAH)_ Idanun BB na kanta duk abunda take sai dai ba kowa ne zai gane hakanba saboda ta tsakanin lashes ensa yake kallonta hannayensa zube cikin aljihunsa. Juyowa KHUBRA tayi da niyyan yiwa ZUHRA magana hannun MAMA dake cikin nata ya motsa,cikin saurin ta juya don tabbatarwa,k'afarta ta sake motsawa sannan sauran wasu sassa na jikinta da suka motsa,a hankali kuma idanunta suka soma bud'ewa. Duk abunda ake babu wanda ya kula da halin da ake ciki,kabbara KHUBRA tayi wanda yasa su saurin matsowa kusa da gadon suna tambayan lafiya,idanun MAMA da suke bud'ewa da ta kafe fuskar MAMAN da kallo ne yasa su kallon abunda takewa irin wannan kallon cikin wani yanayi na jin dad'i gaba d'ayan d'akin suka d'auki kabbara suma,masu hawaye nayi masu murna nayi saboda halin da suke ciki a wannan lokacin na tashin MAMA ba tare da sunyi tsammanin afkuwar hakanba..... 《《》》 Parking sukayi dai² bakin get en gidan suna shirin fitowa BABA MAI GADI ya fito daga gidan da y'ar radio ensa a hannu,kallonsu yayi yana shirin tambayan wanda suka zo nema idanunsa suka sauka kan ASHNA dake kan gaba. "K'aaluu innalillahi wa-inna ilaihi raji'un,me zan gani haka?HAJIYA da gaske kece ko kuwa fatalwa nayi gamo da ita?" Yana tambaya yana kuma had'awa da jaa baya,maimakon tayi magana da fad'a kamar yadda ta saba musu sai yaji sab'anin hakan wanda ya dad'a jefa shi cikin taradaddin anya kuwa itance da gaske? "Nice BABA ba fatalwa bace" Ta fad'a tana d'an murmusawa.. Al-ajabi yake na sauyin da ya gani a tare da ita da yasa shi kasa magana,har suka wuce suna niyyan shiga gidan ya dakatar da su ta hanyar fad'in "Babu kowa cikin gidan HAJIYA" Da sauri suka juyo suna kallonsa,cikin rud'ewa kuma ta fara magana "Ina suka tafi suka barni?dan Allah BABA suna ina ?" "Kiyi hak'uri HAJIYA amma gidan nan ya kai tsawon kwanaki babu kowa cikinsa,HAJIYA ce babu lafiya tana kwance a asibiti cikin mawuyacin halin da ko sanin wanda ke kanta bata iya yi".... Tun kafin ya k'arasa ta fashe da kuka tana fad'in "Ni dama nasan hakan sai ya faru,wayyoo Allah MAMANA dan Allah kada ki mutu ki barni,wayyoo MAMA dan Allah ki tsaya" Surutai iri-iri take wanda bata iya tantance kalmomin da bakinta ke furtawa.. A hankali BIGGY ya matso kusa da BABA yana tambayansa "BABA wane asibiti ne aka kwantar da ita?" "Ehhh tana asibitin MALAM AMINU KANO" BABA ya bashi bayani hatta da d'akin da take a kwance sai da ya musu kwatance,cikin sauri ya figi hannun ASHNA da batama cikin nutsuwarta suka d'auki hanyan asibitin AKTH.... 《《》》 Dai² lokacin da suke tsaka da murnan tashin MAMA cikin sauri KHALEEL da BB suka fice dan nemo likita. Suna cikin d'akin duk sun baibayeta kowa nason ya mata magana,idanunta taketa juyawa tana kallonsu d'aya bayan d'aya. K'ofar aka bud'e da k'arfi cikin sauri duk suka maida hankali gurin dan ganin waye haka ya dokota da k'arfi. Abunda suka gani ne yasa su kowa ya bud'e baki da tsantsan mamaki shimfid'e a fuskokinsu................... *~#TEAM KHUBRA.~* *_#REAL SMASHER._* 💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *11/ʝųlყ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *4⃣2⃣* *'D* akin ya afka ba tare da yayi sallama ba yana muzurai had'e da dubawa ko zai ganota cikin d'akin,amma babu kowa ciki sai LADIYO data mik'e saman gado tana faman shirgar bacci uwa wacce ta sha wani abun. Wata irin tsanarta ce ta dirarwa MALAM BUBA take ya juya ba tare da yayi magana ba,ficewa yayi daga gidan yana ta taraddadin ina yarinyar tasa ta shiga haka. Abubuwa da dama yake tunani akansu da suka faru dashi a y'an watannin da suka wuce wad'anda basu da dad'in ji bare a fad'esu. Dai² bakin wata makarantar primary dake k'auyen ya nemi guri ya zauna nan ya shiga tunanin inda ta shiga da halin da take ciki. Rana ta k'arshe da suka rabu ta fad'o masa da abunda ya janyo rabuwar tasu,kuka ya fashe da shi yana tausaya mata yasan wahala kam da tsanani tana cikinsu a dai² lokacin. Babu mai rarrashinsa sai da yayi mai isarsa sannan ya tsagaita shi kad'ai yake magana da kansa "Allah kaga halin da bayinka suka tsinci kawunansu ya Allah kaine gatanmu bamu da kowa idan ba kaiba,gareka muke neman taimako ya Allah ka k'ara tsaremu a duk inda muka tsinci kawunanmu,Allah ina rok'onka daka tsaremin yarinyata a duk inda take a kuma kowane hali take ciki" Ya jima yana addu'a har sai da yaji zuciyarsa tayi sanyi daga mugun zafin da take masa sannan yayi shiru na wasu y'an mintuna bakinsa kuma har lokacin yana motsawa babu abunda da ke fitowa daga bakinsa face "Astagfirullah wa'atubu ilaih,astagfirullahal azeeym" A dai² lokacin ba komai MALAM BUBA yake tunawa ba sai wani al'amari daya tab'a faruwa shekaru sha tara da suka wuce wanda sune dalilin da yasa yaketa neman gafara,a zuciyarsa yake fad'in "Lallai ya zamemin wajibi na nemeki ko dan neman gafara,a yau Allah ya nunamin abunda ko a mafarki banyi tsammaniba tare da LADIYO,lallai wannan ya tabbatarmin da *BA LAIFINKI BANE"* Wuni guda yana zaune a gurin sallah kad'ai ke tada shi shima da yayi alwala a bakin tap en dake farfajiyar makarantar zai dawo saman varenda a nan zaiyi sallah sannan yaci gaba da zama yana dad'a neman gafarar mahalicci visa kuskuren da yayi shekaru da dama.... 《《》》 K'ofar da aka doko ne da k'arfi yaja hankulansu suka kai dubansu ga k'ofan dan ganin waye haka,kallon ASHNA sukayi wacce idanunta suka gama rinewa saboda tsabar kukan da tayi kafin su iso. Mik'ewa sukayi bakin kowanne na rawa gurin furta sunanta,MAMA dake kwance tsawon kwanaki ko kanta bata san inda yakeba,ganin ASHNA a gabanta dai² lokacin ta mik'e zaune had'e da zare abunda ke bakinta cikin murya k'asa-k'asa ta furta "ASHNA kece zo nan y'ata naji d'umin jikinki kinji y'ata zo maza" Gaba d'ayansu suka kuma juyawa jin maganar MAMA,zaune suka ganta saman gadon da suka barta a kwance,mamaki fal cikin zuk'atansu had'e da farin ciki mara misaltuwa. Da gudu ASHNA ta k'arasa kusa da MAMA,fad'awa tayi jikinta ta saki wani kuka mai ban tausayi kowa sai matse ido yake,hannu MAMA tayiwa KHUBRA alama da tazo kusa da ita,babu musu kuwa ta isa kusa da ita,kamata tayi ta rungume idanun MAMA na fidda hawaye,abun ba k'aramin mamaki ya bawa UMMI,ZUHRA,FATAHIYYA da suke cikin d'akinba farin ciki mara misaltuwa a tare da su,a hankali ZUHRA ta isa kusa dasu tasa hannunta a bayansu itama ta kwantar da kanta bayan ASHNA da KHUBRA tana fidda hawayen jin dad'i. Muryan MAMA ya katse musu kukan da suke "Ku yafe min yarana dan Allah badan ni ba,nasan na cutar da ku na kuma b'ata muku rayuwa ban bi nasiha da kuma burin mahaifinkuba kamar yadda ya barmin wasiyyar kula da kuba,kuyimin aikin gafara in sha Allah haka bazai k'ara faruwaba... KHUBRA ki gafartamin cutar dake da nayi,sanadin haka abubuwa suka sake cukurkud'ewa idan har baki yafemin ba ni kaina bazan tab'a yafewa kainaba".. Kuka ne yaci k'arfin maganar MAMA,inda kafin taci gaba da magana DR ya shigo had'e da sallama bayansa kuma BB ne da KHALEEL,tun kafin DR en yayi magana wasu dattijai suka shigo,nanfa aka fara kallon-kallo tsakaninsu da MAMA dake zaune gefenta kuma ASHNA da KHUBRA ne sai ZUHRA dake kusa da k'afafuwanta. Shi kansa DR en ganinta a zaune sai da abun ya matuk'ar bashi mamaki,baiyi tsammanin ganin hakan a tare da itaba amma sai ya bar hakan a ransa Wayansa ya shiga pressing sannan ya d'orata a kunnensa "Hello DR LEEMA idan babu abunda kike yi ina son ganinki yanzun" Abunda ya fad'a kenan sai number room en da ya shaida mata,cikin y'an mintuna akayi knocking door en,izinin shigowa aka bata ta shigo d'akin dake cike da mutane,nan DR en ya basu umarnin su basu guri yana son ya duba jikin nata. Ficewa sukayi gaba d'aya ya rage daga shi sai DR da kuma MAMA dake zaune har lokacin,da taimakon DR LEEMA suka duba jikin nata inda suka tarar da komai normal,bayan sun gama suka fice,a k'ofan d'akin ya tarar da su nan ya buk'aci ganinsu. "BABA ina ganin ku yafi kamata da ku je don ganawa da likita dan dama ya buk'aci hakan tun kwanakin da suka gabata" "A'a KHALEEL ku en dai kuje tunda kun san dalilin faruwar rashin lafiyar tata,kuma kune y'an boko saboda haka ina ganin zaku fimu fuskantar abunda zai fad'a" 'Dan murmushi yayi had'e da fad'in "To shi kenan BABA amma tunda Allah yasa abun yazo da haka me zai hana muje gaba d'aya,daga nan maji koma mene ya faru da dalilin afkuwar hakan" 'Dan murmushin shima OLD KHALEED yayi sannan ya kama hannun BB yana fad'in "Takwara muje ko?" Wucewa sukayi zuwa office en inda da shigarsu suka nemi guri suka zauna suna masu sauraron abunda zai fito daga bakin DR. Shiru ne ya biyo baya na tsawon wasu mintuna,kafin DR ya sanar musu da yadda jikin nata yake a halin da ake ciki "To yanzu DR nan da zuwa wane lokaci zaku sallameta?" KHALEEL ya tambaya "Ehh to duk da jikin nata sa sauk'i sosai a yanzun zamu rik'eta a nan har nan da tsawon kwanaki biyu zuwa uku". 《《》》 Likkafa taci uban na da a gurin MA'U dan ko tun bayan da likita ya tabbatar mata da babu matsala ta sake kafa sabon kasuwanci da yafi na da a yanzu MA'U da mutane suka sani a baya wannan har ta dame waccen a rashin mutunci da duniyanci,idan abun nata ya motsa mata kwana biyu sai ta haukace yini take tana kan network babu sassauci,su da kansu mazajen nata suna mamakin wannan sauyi nata a y'an kwanakin da hakan ya faru.... Mu dai sai muce Allah ya kyauta na gaba... 《《》》 Kwanaki sun dad'a tafiya inda zuwa yanzun MAMA ta dawo gida kamar ba itace tayi jinyan da bata iya sanin duk wanda ke kantaba. Yau ta kama kowa da kowa yana gida hatta da su BABA KHALEED da suka zo daga JIHAR JIGAWA,gaba d'aya suna zaune bayan gaishe-gaishe da akayi da tsokanar juna,MAMA ta kalli duka jama'ar gurin sannan ta fara magana wanda sai da taja hankulan jama'ar dake gurin gaba d'aya "Da farko kafin na fara cewa komai ina buk'atar neman yafiyarku saboda wasu abubuwa da suka faru wanda a dai² wannan lokaci nake mai burin sanar daku GASKIYAR AL'AMARI'N da ya faru shekaru bakwai da suka faru" Labarin yadda suka rabu da ABBA'NSU BB ta shiga badawa tun daga lokacin da suka fara samun sab'ani har zuwa lokacin da ya bar garin,da yadda suka had'a baki ita da HAJIYA LAURA kan cewa da mutane mutuwa yayi,duk dan gudun kada duniya ta zagesu,gaba d'ayan parlor'n sunyi shiru kowa da abunda ke damunsa da jin wannan al'amari mai matuk'ar rikitarwa da d'aure kai musammanma su BABA KHALEED da basu san da wannan labarinba,shiru mutanen parlor'n sukayi suna jiran jin me kuma zai dad'a fitowa daga bakin wani a gurin. Shiru zuwa tsayin lokaci da haka taron ranar ya watse ba tare da wani ko wata sun sake furta wani abuba saboda zuciyoyinsu na cike da alhini. Bayan tashinsu daga gurin BB tare da KHALEEL suka fice,basu zame ko inaba sai guarding inda suka zauna saman kujerun dake gurin,shiru na d'an lokaci sukama juna kowa na tunani duk da a gurinsu wannan maganar ta MAMA bata wani sasu jin shock kamar sauran mutanen dake parlor'nba kasancewar sun riga da sun san da ita,sai dai a wannan karon suna tunanin mafitane. Bayan shud'ewar mintuna arba'in suna zaman kurame ba tare da wani yayi magana ba da sauri BB ya kalli KHALEEL "Heyyy!MAN ka san me nake tunani kuwa?" Kai KHALEEL ya kad'a masa "Ina tunani ne akan b'acewar ABBANMU gaskiya inaji a jikina babu wanda yasan inda ABBA yake face ABBANKA" Shiru duka sukayi suna kallon juna da sauri sukayi ihu had'e da k'ank'ame juna "Tabbas!kayi gaskiya duk duniya ABBANA ne kad'ai zai iya sanin inda yake,amma me yasa bamu yi wannan tunaninba tun farko sai yanzun???" "Wallahi dai kam MAN na manta ne tun farko,kuma kaima bakayi tunanin hakaba ko?" "Sosaima kuwa sam tunanina bai kawomin haka ba shi yasama ban maka maganar ba" Sai da suka jima a gurin suna shawaran yadda zasu fuskanci ABBAN KHALEEL idan ya diro k'asar tun bayan da ya bar k'asar shima akan wani project da yaje k'asar Singapore na tsawon shekaru uku wanda ya rage masa y'an watanni ya kammala. "To amma MAN baka ganin gara tun yanzun mu tuntub'eshi da maganar,kaga idan suna tare nema zai iya convincing nasa su dawo tare ko kuwa me kace?" BB yayi maganar had'e da kallon KHALEEL yana jiran jin me zai ce masa "Ehh!kumafa shawaran da ka bayarma idan muka bishi hakan zaifi mana" Sai da suka kammala shawaran sannan KHALEEL ya fiddo phone ensa yana dannawa alaman neman wani abu... 《《》》 Shigowarsa gidan zuciyarsa ta sake yin k'unci saboda tunawa da abunda ya faru kwanaki biyar da suka wuce,duk asuba anayin kiran sallah idan ya fice baya tab'a shigowa gidan sai bayan dare ya gama tsalawa alamar babu wanda zai san da zuwansa kenan yake shigowa. Shigowarsa kenan kamar kullum yana k'ok'arin wucewa yaji an rik'o gefen rigarsa,da mugun fushi ya juyo dan ganin waye zai aikata masa haka. LADIYO ce ta rik'e shi sai girgiza take alamar dake nuni da yau ba zaman lafiya kenan,fisgewa yayi tare da nunata da hannu,ba tare da yayi magana ba ya juya zai bar wajen,sake rik'oshi tayi cikin b'acin rai wanda yafi na farko yana juyowa ya d'auketa da mari. Dafe kuncinta tayi tana kuma kallonsa,cikin kaushin murya had'e da sake nunata da hannu "Ke dabbar wace duniyar ce da har zaki rik'e ni? ko kuwa kina tunanin nima baho ne irinki da zaki aikata abu kiyi tsammanin ban saniba To bari kiji duk abunda kike aikatawa ina sane da halin da kike ciki,sai dai abu biyu zuwa uku zan fad'a miki Na farko dai zan fara miki da Allah ya isa da har kike cin amanata kuma a haka kike tunanin ban saniba,kin munafurce ni sannan kin ci amanar hakkin aure to kije ke da Allah,kuma da sannu zaki ga sakamakon tozarta aure da kikayi. Abu na biyu da zan fad'a miki shi ne,tun wuri kuma muna shaida juna duk inda yarinyata take kiyi gaggawar nemo min ita tare da damk'ata a hannuna,idan ba hakaba zan sauya miki hallita sa'annan in damk'aki a hannun hukuma. Abu na uku da zan shaida miki kuma na k'arshe shine daga rana irin ta yau ni MALAM BUBA SA'ADU na sake ki saki uku babu ni babu ke,zaki bar gidannan daga ranar da yarinyata ta dawo hannuna ina fatan kin gane ko?" "Wayyooo Allah ni LADIYO wallahi MALAM baka isa ka sake niba na rantse sai ka zauna dani" "Ke dakata da Allah idan kin manta abunda ya faru shekaru sha tara da suka wuce ni ban manta ba kin gane ko,ni bani da lokacin b'atawa bare har na tuna miki d'anyen hukuncin da kika sani aikatawa saboda sharri da kuma kaidi irin naki" Yana kaiwa nan a zancensa ya fisge rigarsa tare da wucewa ya barta a nan tsaye tana faman taraddadin da tasani bata aikata masa abunda tayi ba tun farko yau ga shi abunda hakan ya jawo,tunani ta lula kan maganarsa.... 《《》》 Sabuwar kulawa KHUBRA ke samu daga gurin MAMA dan yanzun kam ta mai data kamar y'arta data haifa tsakaninta da su ASHNA yanzun babu wata k'iyayya,sai dai kuma har yanzun ta kasa sakin jiki da su kamar yadda su en suke mata shishshigin ganin ta sake da su. Ihu suke tayi suna murnan zuwan UMMI da tazo yanzun babu jimawa,bayan sun gaisheta kowannensu suka fashe daga parlor,hira sosai suke tsakaninsu irin ta k'awaye kamar ba sune da suka jima basa tare ba. "Nikuwa MAMA'N yara da wata alfarma nazo nema gurinki" UMMI ta fad'a tana kallon MAMA dake zaune tana ta faman sakin murmushi kamar ba ita tayi jinya ba "Haba UMMI'N yara wace irin al'farma kuma,ai tsakaninmu ya wuce haka,ki fad'i ko me kike so ni kuma in sha Allah babu abunda zaki nema ki rasa a gurina" "To shi kenan tunda kince haka,dama ba wani abu bane illa ina so ki bani KHUBRA na tafi da ita gidana kinga tunda Allah yasa mukayi aure d'a d'aya kad'ai muka mallaka,ke kuma kina da y'ay'a da yawa,dan Allah ki taimakamin ki bani ita kada kuma kice a'a,saboda ina son y'a mace sai dai Allah bai azurtamu da samun hakan ba" Shiru UMMI tayi tana sauraren MAMA da itanma dai shirun tayi,ko me take tunani ohoo,sai da ta sauke wani dogon ajiyar zuciya sannan ta fara magana "To UMMI ni me zance a kan wannan maganar,ina ganin yaran nan ko da bana raye na tabbatar ke kad'ai ce zaki rik'emin yarana saboda haka ko dukansu kike so a halin yanzu ni babu abunda zance miki" Dad'i sosai UMMI taji dan yadda MAMA tayi maganar ba k'aramin farin ciki tajiba Suna cikin firan ne driver'n gidan yayi sallama had'e da sunkuyawa "HAJIYA dama wani ne yace a fad'a muku kuna da bak'o idan kun bada izini zai shigo" Kallon-kallo akayi tsakanin MAMA da UMMI cikin wani yanayi kuma suka furta "Bak'o kuma daga ina haka?".................... *Ku canki waye a waje yake neman izinin shigowa.....* ☺☺☺ _Kuyi hak'uri da wannan wollah mura ke damuna jikina duk a mace yake shi yasa na kasa yin typing en yadda ya kamata...Luv u oll._ ❤ *~#TEAM KHUBRA.~* *_#REAL SMASHER._* 💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *12/ʝųlყ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~__________________________~* _A kullum kuma a ko wane lokaci ina alfahari daku dan kun rigada kun zame min jinin jiki wanda idan babu ku to lallaine SMASHER bata tab'a moruwa,ina godiya sosai da addu'o'inku gareni,Allah ya bar k'auna.....#1❤ MY PEPs._ *~__________________________~* _Fan's muna baran addu'anku akwai sister enmu da aka nema aka rasa dan Allah ku tayamu addu'a Allah ya bayyana mana ita.._ *~__________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *4⃣3⃣* *K* allon UMMI MAMA tayi kafin ta had'iyi wani irin yahun wahala saboda gaba d'aya tunanin MAMA ya tafi wani nahiya daban. UMMI ce ta kalli driver'n da yake jiran umarni har lokacin tace "Kaje kace masa Bismillah! zai iya shigowa" Da sauri ya fita don isar da sak'on da aka bashi. Har bayan fitansa MAMA bata koma dai² ba saboda firgicin da take ciki wanda ya hanata magana. Da sallama ya shigo cikin shiga ta kamala wanda idan har wanda ya sanshi ya ganshi a cikin wannan kayan zai iya tsammanin ba shi bane wani ne daban,sosai kyaunsa ya dad'a bayyana ga wani classy da ya k'ara,har k'asa ya sunkuya ya gaidasu sannan ya zauna a kan rug,k'afafunsa a tank'washe kamar mai d'aukan darasi,wanda bai sanshiba idan ya kalleshi a wannan shigan zai iya tsammanin dama can haka yake. Shiru cikin parlor'n na wani lokaci,su kuma suna masa kallon rashin sani dan babu wanda ya tab'a ganinsa cikinsu bare ya shaida shi. MAMA ce taga shirun yayi yawa ta fara magana da fad'in "Samari daga ina haka mu nan babu wanda ya shaidaka cikinmu" Kansa ya d'an sosa yana d'an inda-inda dan bai san ta ina zai fara maganaba,kansa a k'asa yana shirin yin magana su BB suka shigo shi da KHALEEL "Da farko dai HAJIYA ni suna na *SADEEQ* wanda wasu daga cikin mutane ke kirana da *BIGGY* na zone domin baku hak'uri tare kuma da neman gafararku bisa abubuwan da suka faru a y'an watanni sannan kuma zuwa wasu satittika da suka shud'e" Kallon mamaki duka suka bishi da shi,inda su KHALEEL suka nemi guri suka zauna don jin abunda zai biyo bayan zancen da yake yi. "A da HAJIYA ni ban kasance cikin mutane masu tausayiba bare imani....." "Subhanallah!" UMMI ta furta "Kai kuwa wane irin mutum ne da har kake furta baka da imani,ka san kuwa ma'anar wanda aka ce bashi da imani? A duk lokacin da aka cewa mutum bashi da imani to tabbas wannan mutumin baya cikin jerin mutane masu imani,saboda ko me ka aikata ka rok'i yafiya daga gurin mahaliccinmu sannan ka nemi yafiyar wad'anda ka zalunta,tabbas ubangiji zai gafarta maka dukkan zunubanka,ina fatan ka gane ko?" Kai ya kad'a mata sannan idanunsa na fidda hawaye kamar mace yace "HAJIYA sam abunda na aikata ba shi da alak'a da abunda kike magana,kamar dai yadda kikaji na ambata ni na kasance ina yin aiki na marasa imani,kamar kuma yadda na kasance cikin marasa tausayi had'e kuma da aiki ga mutane marasa imani" Wani kallo gaba d'aya mutane hud'un dake cikin parlor'n ke masa mai wuyar fassara,gaba d'aya hankulansu na kansa basu da burin daya wuce jin cikakken labarin wannan SARK'AK'IYA. Dad'a duk'ar da kansa yayi k'asa ya goge fuskarsa sannan yaci gaba "HAJIYA ni da kuke gani a da na kasance cikin mutanen da suke yin *GARKUWA* da mutane domin neman wani abu ko kuma asasu sace wasu sannan mutane su yasar wani yanki daban Idan baku mantaba a watannin baya kun nemi y'arku kun rasa wacce kuka jima kuna nema ba tare da kun gantaba Sannan a weeks da suka shud'e kuka sake neman wata kuka rasa,wanda ita kuma ta dawo gida kimanin sati kenan da samunta" "Kaii da Allah dakata kada dai kace mana kai ne k'asurgumin b'arawon da ka sacesu duka" Ba tare da ya kallesuba ya kad'a kai,yin hakan babu b'ata lokaci KHALEEL ya kalli BB daya ke kallon wannan bawan Allah mai matuk'ar k'arfin hali. "Ammafa kayi k'ok'ari kuma ya zama wajibi a jinjina maka saboda bajintar da kayi,a saboda haka ni kuma nayi tunanin karramaka ta hanyar baka lambar yabo..." Da sauri KHALEEL ya kalli BB cikin fad'a yana fad'in "Haba MAN wane irin bajinta kuma?.........wane irin kuma karramawa kake magana ga azzulumi irin wannan?wanda makomarsa bata wuce gidan sark'aba,irin wad'annan mutanen makomarsu ma yaci ace tafi haka muni saboda ayyukansu......" "Ya isa haka SON,me yasa zaka katse shi daga bayanin da yake yi bayan d'umbin nadama da yayi wanda har ya masa jagora akan yazo neman afuwarmu,ina ganin idan har ba dagaske yake ba babu abunda zai kawo shi gurinmu,mu bashi dama muji dame yazo tukuna kafin a yanke masa hukunci....." Maganar da UMMI tayi ita tasa su yin shiru kowanne sai huci yake burinsu bai wuce a kyalesu su sab'a masa halittaba ko samu sassauci,idanun BB sun gama rinewa da b'acin rai ga tarin bak'in cikin dakatar da shi da akayi gurin hukunta wannan k'asurgumin mai laifin dake gabansa,kunnuwansa yasa hannu ya toshe duk dan kada yaji abunda ake fad'a idanunsa a lumshe kamar mai bacci haka ya jingina bayansa a jikin sofa... Kallon matasan samarin BIGGY yayi da suke cike da zafin kai wanda a ganinsu idan har aka barsu da BIGGY to babu abunda zai yi saura a jikinsa.. Sai daya sake kallon mutanen parlor'n sannan yaci gaba "Bisa wannan kuskure dana aikata a rayuwata kuma bisa ga dalilin had'uwata da d'aya daga cikin y'an matan dana sata zuciyata ta kasa nutsuwa wanda har tayi min jagora zuwa alkhairi,itace ta kawo haske cikin rayuwata wanda yayi sanadiyyar dana yanke shawarar dena aikata duk wani laifi dana ke tawa akan hakane na yanke shawarar dawo da ita gida....." Daga nan ya kwashe duk yanda suka yi da ASHNA tun bayan daya sace ta da irin damuwar da ta shiga,har kuma yanda yayi nadama kan aikin nasa ya kuma dawo da ita a ranar da sukaje asibiti shi ne lokacin da suka tarar da MAMA'N ta samu sauk'i,sannan ya k'ara da yadda ya tafi ya bar asibitin wanda a ranar babu wanda ya kula dashi acikin d'akin saboda yadda hankalinsu ya koma kan MAMA... Shiru yayi bayan ya kai nan a zancensa yana jiran ganin matakin da zasu d'auka akansa. "Alhamdulillah!da har haka ya faru kuma muna godiya ga Allah daya sa ka shiryu daga mugun aikin da kake aikatawa,abun farin cikine ace wani ya shiryu ta sanadinmu,wannanma kad'ai ya ishemu alfahari da har haka ta faru Y'anzun shin kana da wata sana'a ne da za kayi bayan dena waccan mummunar sana'ar taka?" "A'a HAJIYA amma dai zan ci gaba da k'ok'arin nema ko dan ganin ban koma wancan sana'ar dana bariba" "To Alhamdulillah da haka ya kasance lallai wannan ya tabbatar mana da cewa da gaske kake yi ka tuba daga wannan d'anyen aiki,abunda zan maka albishir da shi shine idan har ka dena abunda kake gaba d'aya ka kuma yi min alk'awarin bazaka sakeba Ni kuma in sha Allah nayi alk'awarin nema maka aiki,amma abunda nake son ji daga gareka.....shin kayi makaranta ne?" Sai da yayi murmushin jin dad'i sannan ya furta "Ehhhh!HAJIYA nayi karatu rashin aiki ne tun farko da kuma sharrin matar mahaifina ta d'orani a wannan hanyan tun bayan dana rasa mahaifana" "Asshha! Allah ya kiyaye ashema ba hakanan ka fara wannan mummunar sana'ar ba,Allah ya tseratar damu daga sharrin masu sharri amma abu baiyi kyauba Abun da nake so da kai yanzu shine ina so ka kawo min copy na takardunka nan da sati guda kaji ko,sannan kuma kasa a ranka gaba d'ayanmu mun yafe maka abunda kayi mana,Allah kuma ya yafe mana baki d'ayanmu...." "Haba UMMI ta yaya zaki saurin amincewa da maganarsa daga fad'an magana har kin yarda,irin wad'annan mutanen wallahi munafukai ne akwai wani mugun nufi da suke zuwa da shi a zuk'atansu,sai su fake da neman yafiya nan ko wani abu suka hango shi yasa suka lallab'o da sun samu nasara zaki neme su ki rasa...." KHALEEL ya k'are maganar had'e da zabga masa wata uwar harara,wacce shi kam BIGGY baima san yana yiba dan ko kansa a k'asa yake. Hararar shima ya samu daga gurin UMMI sannan ta masa dak'uwa tana fad'in "Ungo naka SON wato kai gaka sarkin fitsararru ko?da nace a bar maganar kai ne bazaka iya yin shiru ba kenan,kana gani d'an uwanka yayi shiru amma kai saboda futsara shi ne zaka ci gaba da magana ko?to Allah yasa na sake jin ka furta wata magana wallahi saina sab'a maka kaji dai na fad'a maka..." Kame bakinsa yayi bai sake yin maganaba duk maganar da UMMI ke yi da BIGGY babu wanda ya kuma ko da tari a cikinsu,har suka kammala maganar da suke,godiya sosai BIGGY yayi musu sannan ya mik'e yayi musu sallama da niyyan komawa,babu wanda ya kulashi tsakanin BB da KHALEEL duk kuwa da yanda ya mik'a musu hannu da zai fita,haka ya fice jiki a salub'e dan sam bai ji dad'in yadda KHALEEL en yake aika masa da kallon tsanaba..... Dai² bakin parlor yana shirin fitowa ta taho a guje tana waiwaye tana ihu da alama akwai wanda ta tsokano karo tayi dashi da sauri ta maida kanta dan ganin mene ta buga haka,idanunsa na kanta duk da lokacin da ya fito zuciyarsa babu dad'i amma yanzun kam da ya ganta yaji dad'i sosai wanda baya misaltuwa,a hankali ya furta "BEAUTY......." Saurin kallonsa tayi dan tunanin inda tasan mai wannan kamannin take sai dai ta kasa ganewa yanzun kam da yayi magana ta rigada ta gama gane ko waye shi en,da sauri ta mik'e daga jikinsa tana fad'in "Kaiii ne?.......me kuma ya kawoka gidanmu?" Dariyama tambayanta ta bashi a hankali kuma ya karkatar da kansa gefe cikin wani irin yanayi yake fad'in "Neman yafiya nazo gurin family enki dama ke kanki" Idanunta ta sake bud'ewa tana k'are masa kallo saboda yadda ya mata kwarjini a yau,kallon sama ba sosai take iyawaba,kanta a kasa zuciyanta na skipping,ga wani feelings da take ji tattare da shi a lokacin,maganar daya mata ne wancan ranar ya fad'o mata a zuciyanta ta furta "Kenan dama maganar dayamin kan zai daina abunda yake yi gaske ne?........To amma wane azzalumi ne yasa shi aikata mana wannan rashin imanin.......?" Duk maganar da ASHNA ke yi batayi tsammanin a fili take yintaba sai da taji ya bata amsa "K'warai kuwa BEAUTY da gaske ne babu k'arya a ciki....Kina son ki san wanda yasani aikata hakan ne?" Yayi tambayan yana kallonta "A'a kawai dai nayi maganar ne amma ba haka nake nufiba" 'Dan murmushi ya sake yi sannan ya furta a hankali "Noo!BEAUTY nasan kina son sani kawai dai kinamin alkunyane ko?" Bata ce komaiba taci gaba da murza ring en dake yatsanta,shi dai BIGGY (SADEEQ) yana ta kallonta duk wani abu da za tayi ji yake tana k'ara burgeshi,musammama wannan y'ar kunya da take nuna masa. "Shin kin san wata mata mai suna HAJIYA LAURA?" Tambayar ta daki kunnen ASHNA wacce bata yi tsammanin jin hakanba,a firgice ta d'ago kanta tana kallonsa,idanunta ne suka cicciko da hawaye cikin rud'ewa tana inda-inda take shirin tambayarsa,ko kafin tayi magana har ya rigata ta hanyar fad'in "To itace bak'ar azzalumar data sa muka sace y'ar uwarki wacce muka yar a k'auyen garin ZAKIRAI,sannan kuma ita ce wacce tasa muka sace ki akan wani buri nata da mu bamu saniba....." Kafin ya kai k'arshen maganarsa tuni ASHNA har tayi fitar burgu ta fad'a cikin parlor tana rusa kuka mai ban tausayi. Shi ko BIGGY dake tsaye ganin hakan da tayi yasa jikinsa dad'a yin sanyi,a hankali ya juya ya bar gidan,yana tafe yana tunanin halin da BEAUTY ke ciki... Fad'awa'nta parlor tana gunjin kuka shi yasa BB bud'e idonsa d'aya yana kallonta,ko kafin yayi magana har sun tsinto maganar ASHNA cikin kuka tana bada labarin abunda BIGGY ya shaida mata yanzun. Da sauri MAMA ta mik'e tana zunduma wani gawurtaccen zagi wanda gaba d'ayansu basu tab'a tsammanin jinsa daga bakinta ba,jikinta sai karkarwa yake kamar wacce ake kad'awa mazari haka ta hau sababi "Lallai HAJIYA LAURA yau kam kin riga da kin gama janyowa kanki k'arshen bala'i,yau ni HAJIYA MURJA zan nuna miki k'arshen colour ena,saina bar miki darasi a rayuwa wanda ko sunana kika ji an ambata zai sa ki dinga gudu dan neman mafaka......ba dai ni kika tab'a ba shi kenan mu zuba mu gani shege ka fasa yau zaki tabbatar da kin tab'o ......... dodo Maza ki shirya yau ga maza nan bisa kanki" Gaba d'aya mutanen parlor'n sun shiga shock idan aka d'auke BB da ya sake maida eyes yayi closing,mamakinsu ya kasa b'oyuwa saboda kowa yasan yadda suke da HAJIYA LAURA duk wani tak'ama da take yi da bazar HAJIYA MURJA take taka rawa,lallai ko yau kam HAJIYA LAURA kin d'ebo ruwan dafa kanki...... 《《》》 Tun bayan da MALAM BUBA ya gama kora mata jawabi take tsaye a nan inda ya barta k'afafunta duk sun mata nauyi wanda ta gagara d'agasu,a gurin ta zube hannunta a ka ta shiga rera kuka babu ji bare gani... Haka MALAM BUBA ya shige d'akinsa nan ko ya shiga jero nafilfili yana dad'a rok'on Allah yafiya bisa kuskuren da ya tafka a baya,sai da dare yayi nisa sosai sannan yayi addu'a ya kuma kwanta yana mai dad'a yin tasbihi ga ubangijin sammai da k'assai. Kwanaki sun dad'a jaa inda a kullum tashin hankalin LADIYO yake dad'a k'aruwa daga lokacin da aka ce mata dare ya kawo kai,zuwa yau kuma babu wani labari dangane da MA'U bare ita kanta KHUBRA da ABBA'NTA yasa LADIYO ta dawo masa da d'iyarsa kamar yadda ya bata umarni. 《《》》 Tun daga ranar da BIGGY yazo gidan har zuwa yau bai sake dawowa ba,wanda zuwa yau an kwashi kwanaki da dama ba tare da ya sake waiwayar gidan ba. A b'angaren ASHNA kuwa ko wane dare da tunani da kuma mafarkin BIGGY take kwana kuma take tashi,ko wane motsawar second ji take kamar za tayi hauka saboda yanda zuciyarta ta damu da shi fiye da tunaninta,tun bata yarda da cewa sonsa take ba har ya kaiga yanzun ta amincewa zuciyarta da son da take masa.. Tafiya tayi nisa a b'angaren zaman KHUBRA a gidansu KHALEEL a yayin da itama ZUHRA tayi tsalle ta dire kan itafa sam bata amince da a sake rabasu ba,nan ta tsaya kai da fata akan sai dai UMMI ta tafi dasu duka,nan ko UMMI tace taji ta gani kuma tana sonsu duka dan haka ta kwashesu duka suka koma gidanta. Kulawa ta musamman suke samu daga gurin UMMI inda ta mai dasu y'ay'a tamkar ita ta haifesu da cikinta,d'aki guda tasa aka ware musu had'e da tsara shi da kayan k'awa wanda idanu bazasu iya tantace ainihin yadda suke ba,bare baki ko hannu su samu damar shaidawa masu sauraro. Rayuwarsu a gidan UMMI kusan za a iya cewa a yanzun sunfi sakewa duba da yadda UMMI ta maidasu kamar wasu k'awayenta,shi yasa suma basa tab'a b'oye mata wani abu daya shige masu duhu,idan ko unguwa zata je zaka tarar dasu tare da ita duk inda ta cire k'afarta to ko nan zasu maida tasu. Zuwa yanzun KHUBRA har ta dad'a washewa ba kamar yadda ta dawo daga garin ZAKIRAI ba,ta k'ara cikowa fatar nan tad'an yi fresh daga muguwar yamutsewar da tayi..... Nema kam kusufa-kusufa akewa HAJIYA LAURA tun daga ranar da HAJIYA MURJA ta samu labarin itace shaid'aniyar data sa aka d'auke mata gudan jininta,wannan dalilin yasa HAJIYA'N cin *ALWASHI* (UMMI AISHA) gurin ganin bayanta... Wannan kenan.......... *~#TEAM KHUBRA.~* *_#REAL SMASHER._* 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *13/ʝųlყ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *4⃣4⃣* *T* un bayan da su KHUBRA suka bar gidan dukkanin wata walwala ta k'are a tare da BB zaman gidanma sam baya masa dad'i bayaga hakama babu wani abinci mai dad'i da suke samu a gidan dama-dama da ace d'aya cikinsu na nan to tabbas da sun samu abinci mai gina jiki musamman ma ace MR'S KHUBRA. A duk lokacin da yaji bazai iyaba sai dai ya shirya tare da ficewa ranan ko gidan UMMI zai nufa a nan zai cika tumbinsa ba shi zai dawo ba sai dare shima sai dai kwanciyan bacci ne zai dawo da shi. Tunda ya san sauran yaran babu abunda suka iya,ko da kuwa ace dafa lipton ne,sam basu san yaya tafasan sa yake ba,wannan lokacin ne kuma da dalilin yasa MAMA ta yanke shawaran ganin ta gyara musu rayuwansu gudun kada a zageta nan gaba (kun jifa fan's). Sosai MAMA ta dage gurin yak'i da son jikinta ta kuma zage damtse gurin ganin hak'anta ya cimma ruwa tare da taimakawar BABA ZUWAIRA da har lokacin take zaune a gidan,dan MAMA sunyi ruwa sunyi tsaki akan baza ta komaba za taci gaba da zama da su har k'arshen rayuwa,duk lokacin da suka taso daga makaranta babu sauran zama a gurinsu gaba d'aya take tusasu a gaba su shiga kitchen bata tab'a rabuwa da su su huta sai dai ko idan akace lokacin sallah yayi ko cin abunci wannan kad'ai ke sawa ta d'aga musu leg. 《《》》 Sanye cikin brown en shirt da black trouser sai wani k'aton Timberland shoe brown colour dake k'afansa,idanunsa sakaye cikin black sun glasses ya ci mazuu,tafiya yake cike da k'asaita kamar kowane lokaci,yana tafiya yana kad'a car keys en dake hannunsa har ya k'araso bakin motan,a hankali ya bud'e sannan ya shige kamar wanda akawa wani abu ya fizgi motan a guje tun kafin ya isa bakin get en yaketa faman doka horn,a guje BABA ya bud'e masa tun kafin ya k'araso,a 220 ya bar wajen wanda ya bar BABA da mamakin irin wannan tuk'i da KHALEED ke yi a yau. Fitansa daga gidan bai zame ko inaba sai gidansu KHALEEL wanda yanzun ya koma YAYA'N KHUBRA da ZUHRA. Motansa na kunna kai cikin farfajiyan gidan idanunsa suka sauka akansu sunata guje-guje,sanye da k'ananan kaya kowacce ta had'e cikin colour en da ranta ke so,k'wallo suke bi a guje suna ihu. Parking yayi a gefe yana kallonsu wanda su sam hankalinsu bai kawo kansa ba,ihun da KHUBRA tayi ne yasa shi dad'a maida hankalinsa kansu,gani yayi ta tsaya tana ta faman dira k'afafu da alama a koi abunda ya faru tsakaninsu,a hankali yayi k'asa da glass en dake side nasa,cikin murya kamar ta mai shirin yin kuka take magana "Allah ban yardaba tun d'azun sai rinto kikemin dan kinga ban iyaba ko...." Dariya sosai ZUHRA ta tsaya tana mata,kallonta KHUBRA tayi ta b'ata fuska had'e da fara matsar idanu tana shirin yin kuka,da gudu ZUHRA ta saki boll en ta nufo inda take,ganin haka yasa KHUBRA felle k'afafunta da gudu ta d'auke kwallon sai jin ihunta ZUHRA tayi tana ta faman doka tsalle kan itama ta ci.. Tsayawa ZUHRA tayi kafin ta juyo tana fad'in "Allah nima ban yardaba ai ojoro kikamin,kuma Allah sai an sake ai ba cin tsakani da Allah bane kikayi" Tsalle KHUBRA taci gaba da yi abunta tanawa ZUHRA gwalo,duk tsallen da take bata san yana kallontaba,waya ya ciro da niyyan kiran KHALEEL,idanunsa kuma har lokacin na kanta a hankali ya danna kiran had'e da d'orata a kunnensa,ring na farko ya d'auka "Ya akayi ne MAN?" "Gani na iso ka fito ina mota...." "Lallai amma kai anyi d'an air gidan surukanka kazo ne da saina fito na maka jagora sannan zaka shiga?" Ya tsina fuska yayi kafin ya bashi amsa "Wa ya sani ne abu a duhu......MALAM idan zaka fito to idan kuma baza ka fitoba na k'ara gaba" "To jarababbe gani nan fitowa kada kayimin masifa ni....." K'it yaji tun kafin ya k'arasa maganan,a hankali ya kalli screen en sannan ya kad'a kansa,shi kad'ai yayi murmushi yana fad'in "Naga ranan da zaka fara yiwa mutane magana da sanyin murya" Da sauri kuma ya fice dan yafi kowa sanin halin mutumin nasa baya son jira. A mota ya same shi ya k'ure volume yana ta faman jin 9ja music da suke playing one bye one daga gurin mawak'a daban-daban. Bud'e motan yayi ya shiga,bayan ya zauna ne ya mik'a masa hannu suka yi musabiha,KHALEEL ne ya katse masa kallonta da yake ta cikin glasses en,juyawa yayi ya kalleshi sannan kuma a hankali ya zare glass en daga idaonsa "MAN lafiya kuwa kake naga idanunka sun sauya colour,anya kuwa ba wani abu ke damunka ba ko jarabar ce ta motsa?" KHALEEL ya tambaya yana kuma dad'a k'ure BB da ido duk dan ya gano damuwar tasa,murmushi yayi masa ta gefe d'aya "Noopp!wani abu ka gani?" "A'a babu komai kawai na ga ka canja ne kamar kana tare da damuwa" Yana magana yana kuma kallonsa duk dan ya gasgata abunda yake damunsan,sai da ya kalli side ensa inda suke ta tsalle-tsallensu sannan ya kalli KHALEEL ya kuma yin wani murmushin "No babu komai......kawai dai ina son......." Sai kuma ya sake yin shiru "Kana son me kuma?" "Uhmmm!nothing.....Kawaifa maganar da mukayi da kai ne kan neman UNCLE a waya da mukayi akan zamu tuntub'e shi ko ya san inda ABBA yake" "Ohhh!kaga kumafa ni wallahi har na mantama da maganar amma in sha Allah kam ya kamata ace tun kafin lokaci ya k'ure mu tuntub'eshi muji me zai ce mana ko....?" "Yeahh!dama dai hakan yafi kamata muyi,amma.....yaushe kake ganin zamu same shi a wayan idan mun kira?......ina nufin wane time ne yake free babu hayaniyan aiki a tare da shi?" "Emmm!ina ganin yanzunma yana gida........yanzunma ya kamata mu jarraba kiran nasa muji" "Okk ka kira mana shi muji ko" Wayan ya jima yana ring ba'a d'aukaba,kamar yadda suka jima suna kira har na wani tsayin lokaci,rashin sa'an samun sane yasa suka hak'ura akan zasu gwada wani lokacin. Shiru dukansu sukayi kamar kurame can kuma KHALEEL ya kalli BB fuskansa da matsanancin farin ciki "MAN ka san wani abu kuwa?" Ba tare da ya jira ya amsa masaba yace "Ko da yakema muje gurin UMMI kawai akwai maganar da nake so muyi da ita kuma sai kana gurin zan iya mata magana" Wani kallo BB yayi masa na rashin fahimta kafin ya bud'e motan ya fita,a baya shima ya bishi suna tafiya dai² zasu shiga parlor KHUBRA ta fello da gudu hannun KHALEEL ta rik'e tana fad'in "YAH KHALEEL dan Allah kayi mana alk'alanci" Tsayawa dukaninsu sukayi da sauri BB ya d'auke kansa daga kallonsu,sai dai yana sauraron abunda suke yi "Haba k'anwata alk'alanci kuma nida ba school of law nayi ba,ina ni ina yin shari'a?" Shagwab'e fuska tayi kamar za tayi kuka cikin muryan tab'ara take fad'in "Shi kenan tunda kaima bazaka goyi bayanaba kun nunamin banbanci,barin je gurin UMMI nasan ita zata goyi da bayana" Hannunta da take k'ok'arin zarewa daga nasa yayi saurin rik'owa yana fad'in "Haba mana k'anwata ta yaya zamu nuna miki bambanci mu mun isa?ko so kike idan UMMI taji yau ta hanamu dinner?" "To ba dai kaima kak'i sauraronaba,ni sake ni nama fasa fad'a maka" "A'aaaaa!ai kam baza ayi haka ba,yi hak'uri ki fad'amin kinji yawwa y'ar k'anwata maza fad'a min..." Ganin yana bata hak'uri yasa ta b'ata fuska sannan ta shiga fad'in "To ba ZUHRA bace wai dan naci kwallon da mukeyi tace ita wai bata yarda ba wai kuma wai rinto nayi mata fa tace,bayan ta fini iyawa" "Aaaaaaa!Haba YAYA ZUHRA ya zaki ce haka bayan kuma ita tayi winning akanki" K'afa ZUHRA ta shiga dirawa itama a k'asa nan da nan sai ga hawaye ya fara layi a fuskarta "Allah tunda kace min YAYA saina fad'awa UMMI dama ai na fad'a maka bana so shi ne kake wani cemin YAYA duk dan kasa na tsufa da wuri" Ihu KHUBRA tayi tana tsalle "Yeeeeee!YAYA ZUHRA....Nima daga yau haka zan na ce miki" "Allah baki isaba kuma idan kika kuma sai munyi fad'a dake" Da sauri ta kwace hannunta daga ruk'on da KHALEEL yayi mata,a guje ta zura sanan ta juyo "An fad'a en YAYA ZUHRA...." Da gudu ta sake d'iba nan ko ZUHRA ta mara mata baya suka shiga zagaye filin gurin sune har cikin Guarding saboda dad'in tsokanar juna da suke yi. A hankali KHALEEL ya juya yana girgiza kai,BB ya kalla ya wani basar kamar baya gurin,fuskar nan ya dad'a d'aureta kamar ba shiba ko lokacin da suka fito a mota dariya ya gama yi yana tsokanar KHLEEL amma yanzun ya wani had'e girar sama da ta k'asa. Ci gaba da tafiya sukayi har lokacin kuma bai wani saki ransaba,cikin parlor'n babu kowa sai TV dake ta faman b'ab'atu ita d'aya,zama sukayi babu wanda ya kula wani a ciki,UMMI ta fito daga corridor en da zai sada ka da stairs en data sakko "A'a SON ashe kuna nan..." "Eh UMMI muna nan amma bamu jima muma da shigowaba" "To yayi kyau kam Allah ya taimaka..." "Ameen.......Ammmmm! UMMI gurinki muka zofa" KHALEEL yayi maganar yana kallon BB da har lokacin bai yi maganaba tun bayan gaisuwa da sukayi da UMMI. "Toh! ina saurarenku ai...Maganar mene kukayi shiru?" Inda-inda KHALEEL ya fara ya kasa magana,kallonsa UMMI ta tsaya yi ganin ya kasa cewa komai ne tayi magana "Lafiya k'alau kuwa kake ta faman inda-inda ka kasa magana?" Kansa ya shiga sosawa wani kallo BB yayi masa mai wuyar fassara kafin ya sake d'auke kansa ya shiga danna phone dake hannusa kamar mai neman wani abu,sai dai maganar da KHALEEL yayi a dai² lokacin ta kusa tarwatsa masa lissafi a burkice ya kalleshi dan son tabbatar da abunda yake fitowa daga bakin KHALEEL en "UMMI damafa kan maganarmu da KHUBRA ne nake son yi miki tuni,tunda ALLAH yasa an ganta UMMI mai zai hana ki sake tuntub'ar MAMA da maganar,kinga idan ABBA ya dawo sai ayi maganar auren ko?" Dariya tayi na jin dad'in maganar da yayi mata cike da farin ciki ta furta "SON kenan banda abunka wannan maganar itace zata sa ka tsaya kana min magana kamar wani mara gaskiya,ka kwantar da hankalinka indai wannan ne,ina so ka sa a ranka kamar nayi mata maganar kuma kamar anyi an gama kaji koh?" "Yawwa UMMINAH shi yasa nake ji dake wollahi,ni iya hakama yau kam kin gama min komai,na gode sosai UMMINAH" Hankalin BB idan ya kai million a wannan lokacin to ya kai k'ololuwa gurin tashi,shi kad'ai lokaci guda har ya nemi farin cikinsa ya rasa,zuciyarsa tayi duhun da baya iya gane me suke cewa a lokacin dan gaba d'aya kunnuwansa suka tafi yajin aiki na wucin gadi,bai san lokacin da ya mik'eba ya shiga neman hanyan fita daga parlor'n,duk maganar da suke masa babu wanda ya iya kulawa haka ya fice motansa ya shiga ya fisgeta fiye da lokacin da yazo gidan,tuk'i kawai yake wanda baimasan inda yake nufaba ikon Allah ne kad'ai ya kaishi gida,MAMA dake parlor taga shigowarsa tana masa magana bai san me take cewa ba bare ya bata amsa,ido itama ta zuba masa har ya wuceta yabi corridor en da zai sada shi da bedroom,da k'arfi yayi banging door en. A saman bed en ya zube zuciyarsa ta gama yin duhun da baya gane komai,da k'arfi yake sauke ajiyan zuciya wanda daga ji kasan bana lafiya bane,idanunsa ya runtse hango lokacin da KHUBRA ta rik'e hannun KHALEEL yayi da yadda take narke masa fuska tana shagwab'a wani b'acin rai ne ya dad'a kawo masa ziyara da ya dad'a hasala shi take ko ya bud'e idanunsa da k'arfi,gaba d'aya d'akin sai juya masa yake yi....... 《《》》 "Ina kika shiga munafuka maza fito dan yau kam ko ani ko ake,imma dai ki nemomin y'ata ko kuma yau na tona miki asirin abunda kikayimin sannan kuma na kaiki gurin mai gari a gaban dubban jama'a nasa a yanke miki hukuncin da bakiyi tsammaniba".. LADIYO da ta b'uya a d'akinta jin shigowar MALAM en ne dama yasa ta zurawa a guje tayi cikin d'aki sannan ta k'ara da rufe k'ofar d'akin nata duk a ganainta ta gujewa had'uwa da MALAM en kan wannan maganar ta al'janar y'ar tasa.. A hankali ta bud'e k'ofar ta fito jikinta a salub'e kamar kazar da kwai ya fashewa sai sink'e kai take yi. "Munafuka algunguma kuma kina jin tsoro ne dama? Da kina tsoro ai da baki aikata duk wani tuggu da kika shiryaba amma kije ke da Allah,sannan ki sani nan da sati guda na baki duk inda KHUBRA take ki gaggauta nemomin ita idan ba hakaba kuma......" Yayi k'wafa kad'ai tare da shigewa d'akinsa ya banko k'ofar Jiki babu k'wari ta mik'e ta koma d'aki,tagumi ta buga da hannayenta duka biyu tana jimamin halin da MA'U ta jefata da kuma irin halin da ita kanta ta jefa kanta,kuka sosai LADIYO take yi tana kuma tsinewa MA'U duk kan damuwar da ta haifar musu,yanzun gashi ta barta a ciki..... _Niko da nake gefe nace kad'anma kika gani,ki jira zuwa nan gaba...._ 《《》》 Tun bayan fitarsa da suketa magana bai saurare suba duk k'ok'arin UMMI bai wuce sanin dalilin canjin da ta gani a tattare da shiba,amma ganin yadda yake tafiya da irin yadda ya fisge daga rik'on da KHALEEL yayi masa a k'ok'arinsa na dakatar da shi daga nufinsa,ta tabbatar ba k'alauba amma sai bata kawo komai a rantaba duba da yanayin da yake ciki kenan lokacin da suka shigo,sai tayi tunanin ko wani abu ke damunsa daban.. FItowansa daga parlor KHALEEL en ya biyoshi duk dan ya dakatar da shi amma inaaa lokacin harya manne motansa,a k'ok'arinsa na yin reverse har round about en dake farfajiyan gidan ya daka da bayan motan amma sam bai kula da hakanba saima ficewa da yayi a 360... Da gudu KHALEEL en shima ya hau motansa ya biyo bayansa ba shi ya kyaleshiba sai bayan da yaga shigarsa gida sannan KHALEEL en ya juya yana kuma jimamin abunda ke damun aminin nasa da ya zame masa kamar wani mai shafar jinnu... 《《》》 Duniyar ta masa k'unci yahuma da k'yar yake iya had'iyansa wanda yake jinsa kamar judar k'asa yake taunawa.. Wayoyinsa dake gefe ne d'aya ciki ta hau kuka,kamar bazai dubaba haka ya banzatar da ita,zuwa wani lokaci daya ji an ci gaba da kiran ya bud'e idanunsa da suka matuk'ar firgitar dani ganin jini kwance cikinsu kamar dama can idanun nasa babu komai cikinsu sai jini.. Ko dubawa baiba ya danna bottom en da baima san me ya dannaba gefen kunnensa ya ajiyeta sannan ya sake maida idonsa ya kulle. Maganar da ya jiyo ne ta cikin wayan yasa shi saurin laluben wayan ba tare da ya kuma bud'e idanunba ya karata a kunnensa. "Hello SON kuna lafiya dai ko?" Sai da yayi k'ok'ari ya saita nutsuwarsa sannan ya iya amsawa "Ehh UNCLE muna lafiya ya k'asar Singapore da aiki?" "Alhamdulillah!kam zamu ce" Shiru sukayi na d'an lokaci kafin UNCLE yace "SON are u there.....?" "Ehhh UNCLE..." "Ok akwai wani abune najika kamar kana cikin damuwa hope dai komai lafiya?" Shiru BB yayi yana dad'a hasaso abunda ya faru d'azun bada jimawaba sannan ya dake "Ehhh to Lafiya dai ba lafiyaba UNCLE" Da sauri UNCLE en yake fad'in "Maza sanar dani abunda yake faruwa son kaji ko kada ka b'oyemin,komai kake ciki ka sanar min nima mahaifine a gurinka kaji ko?" Damuwansa a lokacin ya dad'a kaiwa mak'ura,idanunsa babu abunda suke hasko masa face hotonsu suna rik'e da hannun juna sai dariya suke,da k'yar ya iya furta "ABBA......................." *~#TEAM KHUBRA.~* *_#REAL SMASHER._* 💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *15/ʝųlყ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* _As'alullahal aziiym rabbal arshil aziiym an-yasfiyaki ×7...._ _Cweet sis *SAFIYYA BALA (MOM HANAN)* ina miki fatan samun lafiya mai d'orewa kuma ingantacciya,abunda muka rasa kuma Allah yasa mai ceto ne ranar gone k'iyama,Allah ya bamu hak'uri da juriyan rashinsa..._ *~________________________~* _ALHAMDULILLAH!family nd friends addu'anku a ko wane lokaci garemu tana zama karb'ab'b'iya muna godiya sosai da addu'o'inku,SISTER kuma Allah ya bayyana mana ita,sai dai bata cikin hayyacinta,muna fatan zaku sake taimaka mana da addu'ah akan Allah ya daidaita mata tunaninta...REALLY HEART U MY PEP's 💔..._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *4⃣5⃣* *"SON* me ya faru maza sanar dani,wane ABBA'N kake nufi???" Sai da ya saita kansa zuciyansa kuma na ambaton "Innalillahi wa-inna ilaihi raji'un Allahumma inniy a'uzhubika minal hammi wal-huzn,wal-ajazi wal-kasali,wal-bukhli wal-jubni,wa-dal'iddaini wa-galabatir-rijaal" Take ya d'an fara samun nutsuwa duk da idanunsa na kulle har lokacin,kamar yadda har lokacin bai daina ajiyan zuciyan da yake yi da sauri-sauriba. "UNCLE please dan Allah ka taimakemu idan kasan inda ABBA yake ka sanar damu please........" Daga b'angaren UNCLE en yayi shiru yana sauraron BB,yanayin da ya jishi ya tabbatar da matsala,amma da yake yana sone BB en ya sanar masa ko akwai wata damuwa da zai iya maganceta sai ya sauya salon maganar tasa. "SON nace ka sanarmin da damuwarka idan akwai abunda zan iya to" "Noo!UNCLE babu komai kawai dai muna da buk'atarsa ne kusa damu....behind these ma babu yanda za ayi mu rayu ba tare da shiba,rashinsa tare damu zai haifar mana da matsala a rayuwarmu ko ta b'angaren neman aure,sannan mutane da dama a yanzun sun rigada sun san cewa ABBA ba wai mutuwa yayiba....UNCLE duk duniya a yanzun na tabbata kuma duk inda ABBA'NMU yake ya sanar maka,kuma tabbas kaima UNCLE kasan inda yake....." Yanayin yanda yake magana kad'ai UNCLE ya karanta,shiru duka sukayima juna har na tsawon wani lokaci,jin shirun yayi yawa yasa BB jiki a sanyaye ya furta "Shi kenan UNCLE zamu hak'ura daga nan har zuwa lokacin da ABBA zai ji son ya dawo gida garemu,za kuma muci gaba da addu'ah Allah ya juyo mana da hankalinsa kanmu" Hawaye ne suka ziraro masa ta gefen idanunsa,kasa jurewa ci gaba da magana yayi saboda yadda zuciyarsa ta dad'a yin rauni da sauri ya kashe wayan,saitin zuciyansa yasa hannunsa biyu ya danne bakinsa na ci gaba da motsawa da alama yana addu'ah ne a lokacin... Ko da UNCLE yaji BB ya kashe wayan tsayawa yayi yana kallon screen en,shi da kansa yana tausayawa yaran nan rayuwar da sukeyi ba tare da mahaifinsuba,alhalin kuma yana raye ba wai mutuwa yayi ba. Shi kad'ai a cikin k'ayataccen parlor'n daga inda yake zaune yana hango farfajiyan gidan da yadda tsuntsaye keta sauka da tashi kasancewar glasses ne tsakaninsa da wajen,tunani ya shiga yi na ya zama dole a wannan lokacin ya nunawa aminin nasa b'acin rai muddin yak'i amince masa kan maganar tafiyansu tare.. Niyyan fita yayi amma yanayin daya shiga a lokacin na tausayin halinda yaran ke ciki tsahon shekaru yasa shi fasawa tare da fad'in "Babu inda zani gwarama na jira dawowar ALHAJI SAFWAN en muyi duk wacce za muyi,imma dai ya amince mu koma tare ko kuma na nuna masa kalar nawa fushin a yanzun....." Shi kad'ai idan ya tuna tsayin shekarun da sukayi a k'asar tare tunma lokacin yana zuwa ya koma har aka basu wannan project en na tsayin shekaru uku wanda ya rik'esu a k'asar da yayi masa shamaki da nasa iyalan wanda yake fatan komawa nan bada dad'ewa. Yana tsaka da tunani aka bud'e k'ofa sannan aka maidata aka rufe,har lokacin bai juyaba bare ya damu da ganin wanda ya shigo sanin mutum d'aya ne ke da ikon shigowa haka kai tsaye shi ne dalilin da yasa yak'i juyawan.. Idan ba dan shekaruba gami da jin dad'i da wannan mutumin yake ciki to lallai da nace BB ne ya shigo,saboda tsananin kamanninsa dana hango a fuskar wannan mutimin da ya shigo,bambaci na biyu kuma dana gano wannan yafi BB jiki,wannan su ne dalilan da sukasa nak'i amincewa da wannan mutumin BB ne. "Hey!MR MAN....." A yanda yake ya bawa k'ofan baya ya d'aga masa hannu,har lokacin kuma bashi da niyyan juyawa. Hakan da yayi ya tabbatar masa da akwai matsala,saboda basa haka a tsakaninsu,duk lokacin da d'aya ya fita ya dawo to lallaine zaka tarar da d'ayan yana marhaban da d'an uwansa,brief case ensa ya d'ora saman center table,sannan ya zagayo ya zauna a d'ayan kujeran na kusa da ABBA'N KHALEEL. "Heyy!MR MAN wani abu yana damun kane ka zauna nan,ko kana tunanin wani abune?" Shiru har lokacin bai tanka masaba,shi kuma ABBA yak'i gajiya da tambayansa abunda ke faruwa,daya gaji ne kuma dan kansa ya furta "Allah ya kyauta to,tunda yau kam bani da darajar da za a kulani" Mik'ewa yake shirin yi ganin haka ne yasa ABBA'N KHALEEL ya bud'e baki da k'yar kamar kuma wanda baya son yin magana "SAFWAN koma ka zauna ina son muyi magana da kai ta fahimta" Sai da ya kalleshi tukuna ya tabbatar da abunda ya fad'a hakan yake nufi da shi,sannan ya koma ya zauna yana jiran jin me zai fad'a masa mai muhimmanci haka da ya jawo tun daga dawowarsa yake magana amma yak'i kulashi,maganar da yake yi ne ya katse masa tunani "SAFWAN a yauma zan sake yi maka tuni kan abunda shaid'an yasa kake aikatawa game da iyalinka.....Lokaci ya rigada ya wuce da ya kamata ace ka watsar da duk wani abu daya faru a baya ya kamata ka manta da shi haka,itafa rayuwa itace da kai ba wai kaine da itaba kada ka manta da hakan....Sannan idan kana tunanin kai ka yafe hak'k'inka dake kansu a matsayinsu na iyalinka su suna da girman hak'k'i a kanka wanda ya zama wajibi akanka ka sauke shi tunda har yanzun kana raye kuma kana cikin k'oshin lafiya Ka godewa Allah da ya barka da rai da lafiyarka sannan kuma kayi godiya ga Allah daya baka iyalin da a kullum suke cikin nema da cigiyar inda zasu sameka saboda basu da burin da ya wuce su sake saka a idanunsu Wanda yayi maka laifi daban amma kuma wanda kake hukuntawa daban,matarka ita tayi maka laifi kai kuma kana hukunta y'ay'an da ka haifa,shin bama laifi ne mu?ko kuwa mu za muyi laifi ubangiji ya yafe mana mune baza mu iya yafewa wanda yayi mana ba? Idan har maganar da nake maka a kan iyalinka a lokuta da yawane baka so to tabbas a wannan lokaci a kuma yanzu na yanke hukuncin rabuwa da kai idan har bazaka koma garesuba,kai ba wani aurenba kuma kai baka sawwak'ewa waccan ba,sannan kuma ka fake da sunan kana hukuntata,idan har kasan kana son matarkane to ya zama wajibi ka koma garesu sannan ku gyara rayuwar aurenku,idan ba hakaba kuma wata rana zaka neme ni ka rasa ba kuma zaka sake gani naba saboda zanyi nisa da kai,hukunci yana hannunka ka tsaya kayi tunanin maganata idan bai maka ba kana da damar canjawa amma kada ka manta zab'ar akasin abunda na fad'a nima zan d'auki nawa matakin" Yana kaiwa nan a maganarsa ya mik'e yabar gurin,ba tare da ya bashi damar yin maganaba.... Hannayensa ya d'aga tare da sauke su a kan fuskarsa danshin daya ji ya shafo yasa shi kasa gasgatawa da sauri ya dad'a gogowa dan ya tabbatar da abunda yake zargi,shi da kansa a lokacin ya tabbatar yayi ba dai-daiba,ya kuma yabbatar da tabbas bai zama adaliba idan har wani zai masa laifi ya hukunta wani daban,a yau ya dad'a tabbatar da kuskuren da ya dad'e yana tafkawa,yasan aminin nasa yayi gaskiya tunda suke wannan shi ne karo na farko da maganar aminin nasa ta shige shi fiye da ko wane lokaci. Fuskarsa ya goge kafin ya mik'e ya shige toilet,alwala ya d'auro after kuma ya shiga jera salloli ya jima yana addu'ah bayan ya idar kuma ya d'auka al-k'ur'an yana karantawa saboda yadda zuciyarsa take babu dad'i,sai da yaji zuciyarsa ta koma dai² kafin ya ajiye ya nemi guri ya kwanta akan pray mat en saboda yau kam ji yake bashi da k'arfin mik'ewa ya kwancita a kan bed. Shi kad'ai ya barwa zuciyarsa tunanin hukuncin da ya yanke,ya k'udurce a zuciyarsa ba zai tab'a sanar da kowa abunda ke shimfid'e k'asan zuciyar tasa ba........ *~#TEAM KHUBRA.~* *_#REAL SMASHER._* [6:46PM, 7/19/2018] ®ҽɑӀ $ʍɑՏհҽɾ.💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *19/ʝųlყ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *4⃣6⃣* *K* wanaki sun ci gaba da wucewa inda ko wane b'angare babu dad'i,kowa ka gani da abunda yake damunsa a zuciyansa amma a haka'n ba kowa ne zai fuskanta ba,musamman idan aka ce mutum ba mai kula bane to ko babu lallai yayi saurin gano haka a tare da su. Zuwa wannan lokaci MAMA sun sake d'inkewa da UMMI kamar babu wani abu daya rabasu,a wannan lokacin duk wanda ya ga yanda mu'amalarsu take zaiyi tunanin su en y'an uwane na jini saboda aminci da shak'uwa ta musamman data sake k'ulluwa a tsakaninsu. B'angaren zamansu KHUBRA ko a gidan UMMI basa fuskantar wata matsala saboda yadda UMMI ta maidasu,shi yasa suke rayuwarsu a sake,duk ko ranar da aka ce yau sun zo gidan MAMA wuni suke fira da tsokanar juna ta yadda idan suka tashi komawa sauran mutanen gidan har basa son su tafi su barsu,duk da har wannan lokacin KHUBRA tak'i sakin jikinta da su sosai,idan ka ganta tana fira tana dariya game da tsokana to tabbata da ZUHRA ne,su kansu mutanen gidan har mamakin shak'uwarsu suke. Kamar ko wane lokaci yauma cikin shirin suka fito sai sauri suke,sakkowansu daga saman kenan suka sake jiyo horn da ake ta faman zuba musu,da gudu-gudu suka nufi k'ofan fita a parlor'n da d'an k'arfi KHUBRA ta furta "UMMI mun tafi sai mun dawo...." Tana daga saman stairs en lokacin ta fito daga d'aki kenan tana murmushi tace "To Allah ya dawomin daku lafiya,ku gaishe su kunji,maza kuyi sauri kada YAYA'N naku yayi tafiyarsa...." Ai ko k'arshen maganar bata kaiba sun riga da sun fice,kai ta girgiza sannan ta juya ta koma bed room,dan yanzun kam babu wani abu da zata yi duk sun riga da sun kammala duk wani aiki da ya kamata ace anyi a lokacin. Yana ganin fitowarsu yaci gaba da danna horn,kallon juna suka yi a hankali cikin rad'a ZUHRA tace "Shifa YAH KHALEEL yana da wani abu ko mene nayin horn en bayan gamu mun fito kuma" "Barshi mana yana sane wollah,idan ba so yake mu tashi samaba kam ai saurin da mukema ya isa haka" KHUBRA tayi maganar tana tab'e baki. Duk abunda suke yana kallonsu har suka k'araso,a hankali suka shige inda ZUHRA ke back seat,ita kuma KHUBRA ta shiga gaba,a hankali ya kallesu sannan ya d'auke kansa tare da yiwa motan key suka fice a gidan. Tafiyan kurame sukayi har suka iso cikin gidan,ZUHRA ta fara ficewa ta nufi cikin gida da sauri,KHUBRA dake shirin fita da har ta bud'e k'ofan KHALEEL ya rik'o hannunta,sosai ya rik'e yana murzawa har sai da tayi y'ar k'ara "Dan Allah YAH KHALEEL kayi hak'uri wollahi da zafi" "Ai dama so nake kiji zafin,d'azun gulman me kuke da kuka fito?" Shiru tayi tak'i yin magana sai k'ifta idanu take,a hankali ya matso daidai kunnenta cikin rad'a ya furta "Maza ki ci gaba kinji da biyewa mutane ana yin gulmana dake kinsan idan na kamaki ba da wasa zan mikiba ai...." Batayi maganaba har ta samu ya sassauta rik'on da yayi mata,kusan mintuna biyar suna zaune cikin motan shi bai kyaleta ta ficeba shima kuma bai ficeba,har lokacin kuma hannunsa na rik'e da nata yana ci gaba da murzawa,kome ya tuna kuma da sauri ya saketa jiki a sanyaye itama ta fita ko sallama bata iya yi masaba,sauri take ta zubawa k'afafunta har hard'ewa suke kan tsaban saurin da take kamar wata mara gaskiya... Zaune a guarding hannunsa rik'e da magazine,sanye da fara kar en singlet mai hannu sai farin 3quater,kamar wanda aka ce ya d'ago jin shigowan mota,bin motan yayi da ido,daga inda yake zaune yana hango duk wani abu da yake faruwa tsakaninsu,kallonsu yake zuciyarsa kamar zata fad'o dan tsaban tashin hankalin da yake ciki. Idanunsa har sun soma chanja colour baya ga jinsu da yake suna masa zafi kamar an zuba masa chili a ciki,kansa ya kwantar a baya ganin hakan bai masa ba ya fice daga lambun yana nufan hanyan d'akin da KHUBRA ta zauna kafin b'acewanta,a hankali yasa hannu cikin aljihunsa ya fito da key en sannan ya bud'e k'ofan kamar wanda bashi da kuzari haka ya shiga had'e sa rufe k'ofan,d'akin yake bi da kallo duk tsayin lokacin nan d'akin bai yi k'uraba kamar dama can da mutum a ciki,komai tsaf a d'akin da alama dai BB na kula da d'akin,kwanciya yayi k'asa kan carfet kansa kuma ya d'orashi saman katifan,idanunsa da suka canja launi ya kulle har lokacin jinsa yake kamar ba shiba a fili ya furta "Ya zama dole na d'auki mataki,idan ba hakaba komai zai iya faruwa....." Kamar wacce aka cillo haka ta fad'o cikin parlor'n ko sallama bata iya yiba,akan BABA ZUWAIRA idanunta suka fara sauka da gudu ko ta fad'a jikinta,gaba d'aya kallon mamaki suka bita da shi ita ko kulawa da hakan bata yiba saboda yadda take a firgice sannan ga d'okin ganin BABA ZUWAIRA da suka had'e mata. Dariya suka sa mata wanda ya jawo hankalinta garesu kallonsu tayi tana tsuke fuska kamar mai shirin yin kuka,MAMA dake zaune tana murmushi ta furta "Ya isa haka nan kunga kada kusamin ita kuka kunsan dai hali ko?" Like serious tayi maganan,dalili kenan sa yasa duka suka k'unshe baki amma duk da haka ba wai dainawa sukayi ba.. 'Dan sakin fuska tayi sannan ta gaida MAMA da BABA ZUWAIRA dake ta faman shafa kanta tana murmushi.. Wuni guda cikin gidan amma sam basu ga BB ba,har suka tashi tafiya dan KHALEEL ma daya kawosu bai wani jimaba ya tafi sai yanzun da ya dawo d'aukansu,haka suka tafi basu sashi a idanun suba kuma cikinsu babu wanda ya tambaya yana ina.. ******** Shiri sosai BB ya shiga yi cikin kwanakin ba tare da sanin kowaba dan ganin ya nemama kansa mafita kan abunda ke shirin faruwa da shi,a ganinsa hanya d'aya ce maganin wannan damuwan nasa. Shigowarsa gidan kenan ya zube keys en a saman side drower had'e da wasu takardu,gefe kuma envelop ne sannan luggage daya gama zuba kaya cikinsu. Tsayawa yayi yana kallon room en a hankali ya furta "3 days to go...." 《《》》 Damuwa kam KHALEEL ya shigeta saboda rashin ganin aminin nasa duk kuma lokacin da zai je gidan sam baya ganinsa ko da ko zai wuni a gidan ba zai tab'a ganinsa ba,tun abun bai wani damunsa sosai har yazo abun na matuk'ar damunsa,waya kuwa ko da zai kwana yana kiransa bazai d'aukaba tun yana tura masa text har ya daina. Yanzu'nma da yake zaune cikin parlor kiransa ya gama amma har ta k'araci kukanta ba'a d'aukaba,hak'uri ya bama kansa dan yasan ba d'aukan zaiyiba. Yayi nisa cikin tunani UMMI da fitowarta kenan zata d'auka ruwa a fridge en k'asa ta ganshi zaune,kusa da shi ta isa sannan ta dafa shoulder ensa da yasa ya d'ago. A hankali ya kalleta sannan ya k'irk'iro murmushi da bai kai har zuciba "Lafiya kuwa SON kake....kwana biyu ina yawan ganinka cikin damuwa,kawai dai na kyaleka ne ko zaka yi hankalin sanarmin,amma shiru baka ce min komaiba na zuba maka ido naga iya gudun ruwanka ne kawai,me yasa kake sha'awar sama kanka damuwa?ko kuwa kana sha'awar wani ciwon ya kamaka ne?" Kai ya girgiza mata,ajiyan zuciya yayi sannan a hankali ya furta "Wallahi UMMI ni da KHALEED ne kwanakin nan sam na kasa gane inda ya dosa,idan na kirashi baya d'auka haka ko text na masa ma babu amsa,idan kuma naje gida nemansa bana samunsa,na rasa me yake damunsa da har ya kawo wannan chanjin a tsakanunmu cikin wad'annan kwanakin,na tambaya ko baya nan an cemin babu inda yaje yana garin, na rasa me yasa UMMI...." Yanayin da yake magana ya nuna tabbas abun sosai yake damunsa. "Tun tsahon wane lokaci hakan yake faruwa tsakaninku?" UMMI ta tambaya idanunta kuma na kansa 'Dan d'age kansa yayi alaman tunani "Ammmm!UMMI ina ganin kamar tun ranar dana miki tuni kan neman aurena da KHUBRA ne" Shiru tayi tana tuna ranar da abunda ya faru tsawon watanni biyu kenan da faruwar hakan ai,yanayin da ya nuna har zuwa ficewarsa daga gidan,ita sai yanzunma ta sake yin wani hasashe kan hakan,d'an murmushi tayi sannan ta furta "To Allah ya kyauta amma dai SON kabi komai a hankali kaji ko?Sannan ka tsananta addu'a kan abunda kake nema idan babu alkhairi a tsakaninka da abun cikin sauk'i ubangiji zai maka chanji mafi alkhairi kaji ko?...." "To UMMINA na gode sosai,Allah ya barmin ke" Kansa ta shafa tana murmushi "Maza kaje ka kwanta kaji ko dare yayi,sannan kayi kuma addu'a kafin ka kwanta" "To UMMI sai da safe" Ya fad'a yana bin hanyan bedroom ensa,har ya b'acewa ganinta sannan ta juya tana girgiza kai alamar tausayi dan ta fuskanci abubuwa da dama na shirin faruwa "Lallai ya zama dole na dage da addu'ah kan wannan rikitaccen al'amarin,Allah ya zab'a muku abunda yafi alkhairi baki d'ayanku......" *2 DAY'S LEAP.* Cab en ta parker a k'ofar gidan,cikin shiga ta alfarma kamar baturen daya fito daga k'asar amuruka jikin nan a murje kamar mai rayuwa cikin k'ank'ara,k'afarsa ya sako waje ko kafin ya k'arasa fitowa har cab driver'n ya gama fito masa da luggage's ensa dake bayan booth. Sallamansa yayi sannan yaja luggage's en yana nufan get en gidan,kasancewar safiya ce sosai yasa ya tsaya a dai-dai k'aramar k'ofan knocking ya shiga yi saboda babu lallai ace mutanen gidan sun tashi a wannan lokacin.. Ya d'an jima tsaye kafin aka bud'e k'ofan,kallon tsoro game da mamaki BABA MAI GADI yake binsa da shi wanda yasa shi jaa da baya,murmushi mutumin yayi sannan ya shiga yana jaye da luggage's ensa,shi dai BABA gani yake kamar gamo yayi da wannan sanyin safiyar shi yasa ya kasa motsawa daga inda yake,wucewar mutumin kawai ya gani,faruwar hakan ke da wuya BABA ya shige d'akinsa,cikin seconds da basu fi 3-5 ba ya fito hannunsa d'auke da buta aiko da sauri ya fad'a toilet dake jikin d'akin nasa ta baya... Kallon cikin gidan yake komai yana nan kamar yadda ya barshi sai dai gyara da gidan yake samu wanda ya hana shi tsufa,amma kam kamar yadda yake a wancan lokacin haka ya tarar da komai a mazauninsa.. Fitowansa kenan sanye da train suit da alama zai fita motsa jiki ne,shigowan mutumin yasa shi binsa da kallo tun daga nesa har ya dad'a matsowa kusa da shi kallonsa BB yake jikinsa duk ya saki saboda mutumin da yake gani gaba gare shi gani yake kamar mafarkin da ya saba ne yauma,murmushin da yayi masa ne yasa a hankali ya bud'e baki ya furta "ABBA.............." *~TEAM KHUBRA.~* *_REAL SMASHER._* 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *19/ʝųlყ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *4⃣7⃣* *M* urmushi ya sake yi masa da sauri kuma BB ya isa inda yake tsaye,hannu ABBA yasa ya jawo BB jikinsa,wani feeling's ne suka dinga sauka a cikin jikinsa wanda ya kasa bambance na mene ne a wannan lokacin,da k'yar BB ya iya komawa gefe sannan ya amshi luggage's dake hannun ABBA ya nufi hanyan komawa cikin gida. A dai² lokacin MAMA,BABA ZUWAIRA,ASHNA da FATAHIYYA na kitchen kamar ko yaushe suna had'a break fast daya zama al'ada tun bayan barin su ZUHRA a gidan,duk safiya musamman idan akace weekends to tare suke shiga kitchen. Karafniyarsu a kitchen en ne yasa BB yayi hanyan da sauri bayan ya ajiye luggage's en ABBA a gefe cikin parlor. "MAMA zo kiga wani abun al'ajabi...." Abunda ya fad'a kenan fuskarsa da matsanancin farin ciki,kamar zata tambayeshi kuma ta fasa,hannunta ta wanke sannan ta goge da duster dake saman k'ofa. Fitowa tayi batayi maganaba,ba dan komaiba sai dan yadda taga fuskarsa a sake ba kamar sauran lokaciba da sam basa ganin sakin fuska daga gareshi baya ga haka kuma tasan abunda yake son nuna mata mai girma ne shi yasa tak'i yin maganar.. Tsaye yake ya juya baya hankalinsa nakan wani frame dake d'auke da photo'nsu dukansu sai dai babu HANEEF ajiki,a lokacin KHALEEFA ne k'arami. Yanayin yadda yake tsaye ya juya baya ta kalla ita kam tasan ko daga mafarki ta tashi ba zata kasa gane shiba,jikinta a matuk'ar sanyaye taci gaba da matsowa,kaf jikinta rawa yake saboda bata gama gasgata zatontaba,ita kad'ai take fad'in "Anya kuwa shi ne da gaske ko kuwa gizon da ya sabamin ne yauma.....to amma taya haka zai faru?.......idan har da gizo ne me yasa KHALEED zai kirani.....?" Cikin wani salo ya juyo fuskarsa har lokacin cike da annuri daya gagara b'acewa daga samanta. Still tayi a gurin bakinta bud'e saboda ganin mutumin da batayi tsammaniba a dai-dai lokacin da kuma bata tab'a tunanin faruwar hakan ba. Hawaye ne suka shiga tsere akan fuskarta babu k'ak'k'autawa murya na rawa ta bud'e baki za tayi magana,da sauri ya d'aga mata hannu alaman bai son tace komai,daga haka ya juya tare da bin corridor,jikinta a sanyaye ta goge fuskarta sannan ta kalli BB dake tsaye yana murmushi,ta cikin idanunsa kana iya hango kyallin hawaye da yaketa k'ok'arin dannewa dan ganin baiyi kuka'nba. Murmushi tayi masa itama lokacin da wasu hawayen suka sake biyo baya,da sauri tabi bayan ABBA daya riga ya shige,a bed room enta ta tarar da shi har lokacin yana tsaye bai zaunaba,k'arasowa tayi kanta a k'asa ta sark'e hannayenta,cikin wani irin murya mai cike da nadama da dana sanin abunda ta aikata a baya ta nufi inda yake,kan gwiwoyinta ta zube hannuna rik'e da k'afarsa,hawaye sai ambaliya suke a fuskar MAMA cikin kuka take fad'in "Ka gafartamin abunda nayi maka tsayin wad'annan shekaru,duk da nasan ni mai laifi ce wanda bata cancanci hakan daga gare kaba,amma ba zan gusheba ina neman yafiyarka saboda abunda na aikata maka....Na yarda wallahi ko da mata uku zaka kawo bayana....bazan ce maka a'a ba,na amince...duk duniya bani da burin da ya wuce kace ka yafemin...." Kukane yaci k'arfinta daya sata dole tayi shiru tana shashshek'ar kuka,hannu ya mik'a ya d'agota sai da ya goge mata fuskanta tukun yayi murmushi "Indai har dan wannan ne to kisa a ranki na riga da na jima da yafe miki,fatan ubangiji ya yafe mana baki d'aya,nima kuma ina neman afuwarku na tafiya da nayi na barku tsayin wad'annan shekaru,na yanke hukunci cikin fushi..." Murmushin tayi tana kallonsa sannan a hankali ta furta "Duk laifi nane dana biyewa zuga da rud'in zamani,badan na biyewa son zuciyaba da duk haka bai faruba...." "K'warai kuwa amma tunda yanzun kin gane laifinki komai ai ya wuce....ba kuma nason ki sake taso da wannan maganmaganara kinji ko....?" 'Dan mirmushi tayi hanunta akan fuskarsa take fad'in "Har yanzun kana nan kamar yadda kake.....Zuciyarka mai kyauce da ba kowane ke da irinta ba,na godewa Allah daya bani miji irinka mai saurin yafiya da kuma tausayi,sannan kuma na godema mijina daya yafe min laifin da na aikata masa baka rik'e niba....." Wasu hawayen ne suka kuma gangarowa,da sauri ya girgiza mata kai fuskarsa kuma ya d'an had'eta alama'n baya so. Hannu tasa tayi saurin gogewa tana k'irk'irar murmushi "Ina yarana suke sam banji alamunsu ba" "Ka huta tukun kafin nan sai na kirawo maka su......" "A'a bana son jin wannan magana sam...yanzun nake son ganin sanyin idaniyata maza a kiramin su,yanzun zan fito mu gana dasu" Murmushi tayi "An gama ranka shi dad'e..." Tana fad'in haka tayi hanyan fita daga d'akin kuma tana waiwayensa..... 《《》》 Da sauri UMMI ta fito daga bedroom tana kiran KHUBRA da ZUHRA,Fitowa sukayi daga kitchen suna amsawa. "Yawwa y'an albarka maza kuyi sauri ku shirya mana breakfast UNCLE yana hanya,yanzun ya kirani yake fad'amin ya kusa k'arasowa gida....UNCLE yayi mana zuwan bazata wollahi..." "UMMI ai har mun jima da kammalawa ma" Kallonsu tayi tana murmushi "Da kyau y'an matana Allah yayi muku albarka" Amsawa sukayi da ameen,kafun su juya wani kiran ya dad'a shigowa wayan dake hannunta,kallon wayan tayi da sauri kuma ta d'aga ganin MAMA ce,kafin tayi magana har ta rigata ko gaisawa ba suyiba ta ji MAMA'N tana fad'in "UMMI'N YARA dan Allah ki turomin su ZUHRA yanzun KHALEEL ya kawosu...." "To Allah dai yasa lafiya kike nemansu da wannan farar safiyar" "Lafiya k'alau wallahi....ai da labari amma sai mun had'u...." Yanda tayi magana ya tabbatar mata da abunda ta fad'a wani abune na farin ciki yake shirin faruwa koma ya faru. "To Allah ya sadamu da alkhairi..." Da sauri MAMA ta amsa da ameen tana y'ar dariya,ita dai UMMI sai mamaki take kome ya faru haka MAMA take neman yaran da wannan safiyar ohoooo,sai dai sun had'un kamar yadda ta fad'a taji koma mene... "Kuna ina kuma.....?" Da sauri suka lek'o daga kitchen "Yawwa tunda kun gama maza kuzo ku shirya zaku je gidan MAMA..." Tsalle sukayi suka rik'e juna kamar wad'anda suka jima basu jeba.. "Bari na tashi YAYA'NKU sai ya kaiku...saura idan kun shiga d'aki kada kuyi sauri ku fito kunji....kun dai san halinsa..." Tsere suka shiga yi suna dariya,itama UMMI murmushi tayi tana binsu da kallon sha'awa.. *SOME HOUR'S LEFT.* Suka shigo cikin parlor'n mutanen gidan gaba d'aya suna parlor,abun mamaki kamar ana wani taro na musamman,shigowa suka yi suna kalle-kalle sannan suka gaida MAMA dake zaune kusa da ABBA ta sha ado,idan ba wanda yasan MAMA ba a wannan lokacin babu tabbas ya ganeta saboda yanda ta koma kamar wata basarakiya.. Fuskarta cike da annuri take kallonsu Kusa da ASHNA suka zauna cikin rad'a ZUHRA tace "ASHNA bak'o mukayi ne kuma yau?" Tana dariya tace "Ke dillah ABBA ne ya dawofa baki gane shiba ne?" Ido ta zaro tana fad'in "ABBA fa kikace....dan Allah da gaske ko wasa?" Hararar wasa tayi mata sannan ta dad'a sunkuyowa a hankali ta furta "Banda abunki idan ba ABBA bane to wane zai zauna kusa da MAMA haka wanda ba muharraminta ba...." "Ehhh to kumafa hakane...." Bakinta a bud'e ta d'ago "ABBA barka da dawowa" Gaba d'aya parlor'n aka sa mata dariya,kallonsu tayi d'aya bayan d'aya tana sunk'e kai jikin KHUBRA dake mata dariya itama "Sai da kika tambaya sannan kika gane ni kenan" Dariya tayi bata iya yin maganaba,hannu ya bud'e mata a hankali kuwa ta mik'e ta nufi gurinsa,alama yayiwa KHUBRA da tazo saboda MAMA tayi masa bayaninta tun kafin ya ganta,sai dai kuma ganinta yasa shi jin wani abu game da itan,rungumesu yayi gaba d'aya ko sukayi luf a jikinsa dama ZUHRA ma ba bayaba ce gurin son jiki da ita da KHUBRA shi yasa amintar tasu tazo d'aya.. Nan a parlor suka shiririce ranar idan kaga sun motsa daga gurin to sallah zasuyi sai ko cin abinci abunda ke tashinsu kenan. Wajejen bayan salla'n Asr motan su KHALEEL ta dad'a kunno kai,dan dama daya kawo su bai shigaba ya koma gida,sai yanzun da ABBA'NSA yasa shi kawosu shi da UMMI... Anyi gaishe-gaishe UNCLE na shirin yin magana ABBA ya dakatar dashi ta hanyar yi masa inkiya.. Hira sosai ta yaushe rabo ake tsakaninsu duk wanda ya kallesu sai sun bashi sha'awa ganin yadda family biyu suka had'e kamar guda d'aya. Sai dare suka shirya komawa gida,ZUHRA da KHUBRA na shirin bin UMMI ta daka tar dasu,gefe ta jasu saboda tana son yin magana da su "Kunga yau ABBA ya dawo ko? to abunda nake so da ku,ku zauna kuyi masa wannan girke-girken naku shima kunji ko?....idan ya so bayan kun gama yi masa barka da dawowa da kaina zan dawo na d'aukeku kunji ko y'an albarka..." Cike da murna ko dan dama kawai sunyi hakan ne dan kada ace sunyi ba dai-daba,sallama suka mata sannan suka juya.. UNCLE rik'e da hannun ABBA suma suna gefe UNCLE en ya furta "Bansan dalilin da yasa kak'i yarda ayi maganar abunda ya faru ba.....ko mene ne ma'anar hanawan da kayi?" "Uhmmm!kasan shi sha'ani irin wannan ba a buk'atar tado shi,sannan ba a buk'atar yaro ya sanshi saboda zai jima yana kallonka a matsayin mai laifi....Bayan hakama bana son yin abunda yarana zasu tsaneni.." Jinjina kai UNCLE yayi sannan sukayi musabiha tare da sallama da juna suka d'auki hanyan komawa gida suna d'agama juna hannu cike da farin ciki mara misaltuwa... Tun daga ranar da ABBA ya dawo su KHUBRA ke aikin dafawa da saukewa har tsayin kwanaki bakwai,a ranar ne kuma suke sa ran zuwan UMMI don komawa gida,sosai ABBA ke jinjina musu namijin k'ok'arin da suke,sboda duk girkin da za ayi a gidan idan ya tambaya amsar bata wuce ta kullum wato *KHUBRA da *ZURA* ,idan ko akace ABBA na zaune a parlor haka zasu kewayeshi kowa na bashi labari har rasa na wa zai saurara yake saboda hayaniyansu bata bari yaji labaran nasu,su kuma bazasu bari wani ya bada nashi sannan wanima yayiba,a'a sai dai suce duka zai saurara.... 《《》》 A b'angarensu KHALEEL kuwa tun da ABBA'NSA ya dawo bashi da wani abokin hira ko shawara daya wuce ABBA'NSA. Zuwa yanzun ABBA'N yasan da maganar KHALEEL,yanzun hakama maganar tafiya neman aurenta ake wanda ABBA ya sanar da ABBA'NSU BB zuwansu,da suka gama yanke shawaran zuwa nemo aurenta gurin mahaifinta... Koda ABBA yasa MAMA ta tambayi KHUBRA yadda zasu samu ganin mahaifinta kuka tasa mata,sai da MAMA tayi aikin lallashi da taimakon ZUHRA da kuma banbaki sannan tayi shiru. "Ni bansan me zanceba akan haka...." Abunda ya fito daga bakin KHUBRA kenan fuskarta a had'e Kallonta kawai ZUHRA tayi "To banda abunki SISTER sumafa iyaye suna da hakki akanki ko dan sanin inda kike rayuwa da sanin matsayin rayuwarki....yanzun duk son da kikewa ABBA zaki so barinsa?ko kuwa zaki so barinsa cikin mawuyacin hali? Yanzu baza kiso ganin saba da sanin yana raye ko kuwa akasin haka ba?" A tsorace ta kalli ZUHRA dake magana,ita kuma ganin yanayinta yasa tace "Ehhhh!ko kina so ace haka ya faru da ABBA'N?....." Kaita girgiza da sauri hawaye yana sakkowa kan fuskarta jin ta ambaci mutuwa "Nooo!bafa kuka za kiyiba....idan har kina son ganinsa to kiyi k'ok'arin bada address na gidanku kinji sister'na" Cikin sheshshek'ar kuka ta fara magana "Bazan iya bada kwatance ba....." Zaro ido ZUHRA tayi MAMA kuma tana gefe tana jinsu tak'i magana "To sai me kenan?" "Zan iya gane gidan da kaina amma bazan iya bada kwatance ba" Sai lokacin suka gane abunda take nufi,aiko cike da jin dad'i ZUHRA ta furata "MAMA idan zasu tafi nima zan bisu...Kinji?" Dan tasan abunda ABBA zai ce kenan wato a tafi da KHUBRA.. Nan ko ASHNA ma tace "Nima haka MAMA....." FATAHIYYA ta kallesu "Nima kinji MAMA zani..." Dariya MAMA tayi "To shi kenan...kuje ku fad'awa ABBA idan ya amince sai ku bisu......" Kafin ta rufe baki har FATAHIYYA ta fice dan tambayan ABBA.... ********* Tun da sanyin safiya aka hau shirin tafiya garin na KASHIN DILA dake cikin K'ARAMA HUKUMAR KIRIKASAMMA dake cikin HA'DEJIA a jihar JIGAWA... Shirin tafiya ya kankama a wajen ABBA,UNCLE dama jagororin tafiyan wato BB da KHALEEL,sai sauran yaran wato ZUHRA,KHUBRA,ASHNA da FATAHIYYA da suke seat en baya,jikin KHUBRA yayi sanyi sosai tunda taga sun d'auki hanya,sai take ganin kamar yaune aka rabota da mahaifinta,kanta ta kwantar jikin ZUHRA zuciyarta babu dad'i,a haka da take kwance take matse idanunta tana hawaye... BB da KHALEEL na gaba amma babu wata hira da suke sai dai idan KHALEEL yayi magana BB ya Amasa masa da "Eh ko A'a".... 《《》》 "Kina ina maza fito yau ba sai gobeba wollahi sai mai gari ya shiga tsakaninmu,dole ki nemomin inda y'ata take..." Rab'e-rab'e take tana bin hanya,tana fitowa ko ABBA ya maka mata wata uwar harara da shi kad'ai ya san ma'anarta,sai kuma ita da akayi dominta Jiki na rawa baki na b'ari take fad'in "Dan Allah dan sonka da ma'aiki kayi min rai MALAM....... dan Allah ka k'aramin lokaci....Wallahi zan nemota duk inda take...." "Ke rufemin baki mak'aryaciya munafuka kawai....Har tsawon wane lokaci kuma zan ci gaba da zaman jira....Wallahi yau sai na tona miki asiri ko kuma ki fitomin da inda take...." "Wallahi MALAM naji zan nemota amma kayimin rai dan Allah" K'afafunta zube a k'asa take wannan bayanin wanda babu abunda ke fitowa tsakaninta da MALAM BUBA sai uwar harara da yake sakar mata babu k'ak'k'autawa... "Kin san Allah yau kam ba zan kyalekiba,sai mun dangana da gurin mai gari kuma tabbas sai kin karb'i hukunci a yau ba gobeba....." Cakumota yayi ya mik'ar tsaye yana shirin yin hanyan k'ofar gidan da ita yana ingizata gaba "Tsohuwar munafuka algunguma muje....." Ko rufe bakinsa baiba tsayuwan mota ya dakatar da shi,da sauri ya nufi hanyan zaure yana son dubawa,har lokacin kuma LADIYO na chafe a hannunsa........ *~#TEAM KHUBRA.~* *_#REAL SMASHER._* 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *21/ʝųlყ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *4⃣8⃣* *K'* atuwar motar da tayi parking a k'ofar gidan nasa yake bi da kallo game da tsantsan mamaki a zuciyarsa yake fad'in "Wannan kam sunyi makuwa da alama gidan mai gari suke nema....." Bai gama tunaninba mutanen ciki suka shiga fitowa d'aya bayan d'aya,har lokacin ABBA'N KHUBRA mamaki ne shimfid'e a saman fuskarsa saboda rashin sani wanda ake cewa ''yafi dare duhu''. KHUBRA da take kusan ta k'arshen fitowa daga motan,idanunta suka sauka kan mahaifinta da ako wane lokaci shi ne farin cikinta,nan ko ta kwasa a guje bata tsaya wata-wataba ta ruk'unk'umeshi,kukantane ya bayyana inda shi kuma ABBA ganin wannan al'amari yasa shi fad'in "Y'ar nan yi maza ki sake ni kada ki jawomin abunda za a jefeni....kina yiwa Allah ki sakeni tun kafin labari ya isa kunnen mai gari...." Idanunta da suka gama jik'ewa da ruwan hawaye ta d'ago tana kallonsa har lokacin kuma wasu na ci gaba da sakkowa "Alhamdulillahil-laziiy bii ni'imatihi tatimmus-salihaat!!!...." Abunda bakin ABBA'N nata yaketa furtawa kenan har lokacin kuma ya gagara sakinta saima dad'a k'ank'ameta da yayi kamar wanda akace za a rabasu har abada. "UWATA ke ce ko kuwa gizo kikemin kamar yadda kika saba zuwamin...?" ABBA'N nata ya tambaya cike da rashin gasgatawa,saboda a ganinsa a ko wane irin lokaci zata iya b'acewa daga gurin. "ABBA nice ba gizo bane..." Godiya kawai yakewa Allah daya bayyana masa y'ar tasa kwaya d'aya tal. ABBA'N BB ne ya matso kusa dasu hannunsa na nuna MALAM BUBA da shi sam ma bai kula ta kansuba y'arsa ce kad'ai abunda idanuwansa ke hango masa,da k'yar ABBA ya harhad'a kalmomin yana fad'in "M.A....L..A..M......BU....BU...BUBA....." A d'an firgice ABBA'N KHUBRA ya d'ago kansa yana kallon inda aka ambaci sunansa,kallonsa yake like no other yana son tuno inda ya sanshi,amma sam k'wak'walwarsa ta gagara tunawa da abunda yake son ganewar tattare da wannan d'an gayun mutumin. "Nasan da wuya ka iya shaidani amma da zaka kalleni sosai tabbas zaka iya tuna fuskata..." ABBA ya fad'a yana murmushi,aiko kamar wanda aka bawa wani gagarumin aiki ya k'ure shi da idanu duk da ya kasa tunawar hakan baisa ya hak'ura ya daina kallon ABBA'N BB ba.. "A gaskiya ALHAJI ban shaidakaba,sai dai ko kamin k'arin bayani la-Allah sai na iya tunawa" Sai da ya saki wani k'ayataccen murmushi wanda ke bayyana kyau da kuma zallan hutu da wannan bawan Allah ke ciki sannan ya furta "Ehhh! to ina ganin mu zauna tukun dan maganar tamu bata buk'atar muyita a haka..." LADIYO na gefe rakub'e a zaure tana lek'e dan tun bayan da ta samu MALAM en ya saketa tayi zaraf ta shige had'eda lab'ewa tana lek'en wad'annan turawan bak'in. Duru-duru MALAM en ya shiga yi na neman abun da zai shimfid'a musu su zauna,kafin yayi yunk'urin yin wani abu LADIYO tayi zaraf ta fito tana fad'in "MALAM ai da ka kaisu cikin gidan ko dan nan yayi kan hanya..." Wata uwar harara ya sake aika mata wacce take nuni da 'idan kika sakemin shishshigi zanyi maganinki,a fusace ya wuceta dan shi kam gare shi ya tsani ko da ganinta bare har wata magana ta shiga tsakaninsu. K'atuwar tabarma ya shimfid'a musu sannan ya shiga fad'in "Bismillah...!!!" Gaba d'aya ko suka nemi guri suka zauna,LADIYO da MALAM ya barta tsaye da sakakken jiki ta nemi guri daga can gefe ta rakab'e,a inda kuma tayiwa kunnuwanta matsuguni a tsakiyar mutanen da takewa kallon daga wata k'asar suka zo,musamman y'an matan da har yanzu babu wacce ta shaida hatta kuwa da KHUBRA dake kusa da ABBA'NTA ta jingina dashi,idan ta kalleshi sai tayi murmushi a zuciyarta take fad'in "Yau nima na samu y'anci gani kusa da mahaifina...." Abu d'aya zai iya sawa kayi saurin gano b'acewar annurin dake kan fuskarta a wannan lokacin,ba komai bane kuwa face tunanin MAHAIFIYARTA da bata tab'a ganiba. Muryoyinsu ne suka katse mata tunani inda suke ta faman gaishe-gaishe da tambayan juna iyali,bayan nan kuma gurin yayi d'an shiru na wucin gadi kafin ABBA'N KHALEEL yayi addu'ah. Nan kuma aka koma kan ainihin maganar da ta shigo dasu,ABBA ya sake kallon MALAM BUBA da yake jiran k'arin bayani daga bakinsa,kamar yadda suma sauran jama'ar gurin suke sauraron jin me zai biyo baya. "Nasan gaba d'ayanku kunyi mamaki musamman dana nuna nasan MALAM BUBA ko?......" Nan suka hau amsawa da "Hakane....!" "To Alhamdulillah! yanzun zaku ji yadda akayi na sanshi duk da dai shi bai shaidaniba..." Kallonsu ya sake yi d'aya da d'aya,KHUBRA kuwa murna take yi jin ABBA'NSU ZUHRA yasan ABBA'NTA,fuskarta sai annuri ke fita "Ni dai dai farko suna na SAFWAN kuma ni haifaffen garin DUTSE ne ta nan jihar JIGAWA" Kallonsa sosai MALAM ya sakeyi jin sunan daya ambata,kamaninsa ya shiga hangowa ko tantama ba yayi shi ne dai wanda ya sani shekara da shekaru da suka gabata.. "Tabbas wallahi shi ne!....Shi ne....SAFWAN...." Sai kuma ABBA'N KHUBRA ya fashe da kuka da alama akwai wani abu da yake damunsa wanda ya tuna a dai² lokacin. Da k'yar suka lallasheshi yayi shiru,inda gaba d'aya sauran jama'ar gurin suke kallonsu,saboda yadda suka sasu a duhu "Tabbas sai yanzu na shaidaka...." Sabuwar gaisuwa suka sake da tambayar bayan rabuwa. ABBA'N KHALEEL ya kalli ALHAJI SAFWAN yana fad'in "To ALHAJI mu kam kun samu a duhu,bamu fahimci abunda kuke nufiba.....dama kun san juna ne kam ko yaya abun yake....?" Kai ABBA ya girgiza masa kafin yayi magana MALAM BUBA har ya rigashi "K'warai kuwa mun jima da sanin juna...kamar dai yadda kuka gani yanzun zan yi muku bayanin alak'ar dake tsakanina da SAFWAN.... Ni dai da farko suna na ABUBAKAR SA'ADU wanda mafi yawancin jama'a suka sani da MALAM BUBA kamar yadda na taso da wannan suna....alak'ar dake tsakaninmu kuwa ita ce....... 《《》》 Ciwo ne ya soma cin k'arfinta tun bayan zuwanta asibiti da likita ya sanar mata komai lafiya bata sake yunk'urin komawaba,jikinta duk babu kuzari a yanayin yadda take jinsa babban dalili kenan da yasa yau d'in ta shiga shiri babu ji bare gani na ganin ta koma asibitin tunda ciwon yaci k'arfinta.. Tafiya kawai take amma da tayi tayi sai ta huta,saboda rashin kuzari duba da yadda kwanakin take fama da amai da gudawa. Layin karb'an kati tabi bayan jira da tayi na wani lokaci sannan aka sallameta,hannunta rik'e da katin ta nufi office en likitanta na wancan lokacin. Shiganta office en ta nemi guri ta zauna kan kujera,katin ya amsa idanunsa sanye da glasses ya kalleta yana mata tambayoyin abunda ke damunta.. A hankali take motsa bakinta saboda ina ganin kamar bakin natama ya tafi yajin aiki had'e da sauran gangan jikinta.. Idanunsa na kanta har ta k'are bayaninta sannan yayi y'an rubuce-rubuce,bayan y'an mintuna kuma ya sake d'agowa yana mata bayanin za taje tayi test a yau ta kawo masa,amsa tayi ta fice daga office en kamar wancan lokacin,bata zame ko inaba sai laboratory na asibitin.Bayan an d'ibi jininta ta zauna jiran fitowan sakamako a nan. Mintuna sun sake shud'ewa inda wata nurse ta hau kiran sunanta aiko nan MA'U ta mik'e da k'yar tana nufarta Wani kallo nurse en ta mata sannan ta mik'o mata sakamakon gwajin tana yatsina fuska,haka ta karb'a sannan ta kamo hanyan dawowa gurin likita danjin me kuma sakamakon nata zai nuna a karo na biyu. Shigowarta office en ta tarar da shi yana waya kan dole ta tsaya jiransa har ya gama,sannan ya amshi takardar dake hannunta,zaro farar takardar yayi da take ninke a cikin envelope ya warware,abunda idanunsa suka fara tozali da shi shine yanda gwajin jininta ya koma *POSITIVE* maimakon *NEGATIVE* wannan shi ne abunda ya tabbatar masa da matar na d'auke da cutar da yake hasashe,ajiyan zuciya yayi sannan ya maida takardar ma'adaninta,cikin sanyin murya ya shiga yi mata nasiha kan yarda da *K'ADDARA* da kuma karb'arta ta kowane fuska tazo maka mai kyau ne ko akasin haka,ita dai MA'U ido ne nata babu baki,sam ta kasa gane inda wannan tatsuniya ta likita ke tafiya duk ta kafeshi da idanu "Likita nifa har yanzun ban gane ma'anar wannan wa'azin nakaba ,kawai idan zaka sanarmin abunda ke faruwa to,idan kuma bazaka fad'a ba to ka sallameni dan na gaji da zaman gurin nan" Kallonta kawai yayi jin yadda take magana cikin kaushin murya a ransa ya furta "Lallai wato bata san meke faruwa ba amma takemin irin wannan maganar....aiko zaki san ni kikewa magana haka" Yayi niyyan sanar da ita cikin ruwan sanyi amma maganarta tasa shi had'e giran sama dana k'asa ya shiga fad'in "HAJIYA sakamakon gwajin da aka miki ya tabbatar mana da kina d'auke da cuta me karya garkuwa'n jiki wato *HIV* kenan kamar yadda muke kiranta a turance,wanda a hausa kuma muke kiranta da *K'ANJAMAUU*......." 《《》》 Hannunsa d'auke da envelope yana tafiya yana kare fuskarsa saboda zafin rana dake damunsa,ci gaba da kallon hanya yake saboda hangen abun hawa da zai d'auke shi a lokacin,da k'yar ya samu NAPEP ya fad'a masa inda zashi,tafiyar mintuna k'alilan ta kawosu bakin k'aton get en,kud'i ya fiddo ya sallami mai NAPEP en sannan ya tura get en ya shiga. Tun daga harabar gidan nake kallon gurin kamar na sanshi haka wani lokaci daya gabata,cikin sauri ya shige k'ofar da zata sadashi da babban parlor na k'asa,shigowarsa ya tarar dasu sun baje kayan shaye-shaye wasu da kwalabe wasu kuma sai had'awa sama hazo suke. "Innalillahi wa-inna ilaihi raji'un!!" Abunda ya fara fitowa daga bakinsa kenan,cikin fushi ya isa gurin baiyi wata-wataba ya shiga fashe kwalaben a k'asa cikin fad'a yake fad'in "Ban fad'a muku kada wanda ya sake yimin shaye-shaye a gida ba?.....ko kuwa so kuke ayimin cunen y'an drugs? To wallahi yau kam kunyi na k'arshe dan dukanku sai kun barmin gida...gara kusan inda dare yayi muku,nima na samu Hutu da nutsuwar zuciya.." "SO.....SO...SORRY OGAAA...." Wani yaronsa daya sha yayi mankas ya fad'a idanunsa na rufewa da bud'ewa "In...sh...sh...sha....Allahu ba zaka sake kamamu da wannan laifinba.." Tsaki yayi ya wuce hanyan stairs a ransa yake fad'in "Ya zama dole akaina ko dai ku chanja hali ko kuma dukanku dole na rabu daku" Kafin ya k'arasa haurawa saman wayansa dake aljihu ta soma k'ara da sauri ko ya zarota ganin bak'uwar number har zai fasa d'auka wata zuciyar tace "Ina kai ina k'in d'aukan bak'uwar number,ai kawai ka d'auka wata kila ko cikin guraren da ka kai takardunkane aka dace ka samu aikin da kake nema...." Bai ka'arasa tunaninba yayi saurin d'auka had'eda karata a kunne,cikin harshen nasara daga gefen da aka kira shi ake fad'in "Ko kaine SADEEQ MUHAMMAD?" Cikin hanzari har yana had'awa da girgiza kai BIGGY ya amsa da eh shi ne.. "Muna nemanka ranar monday a ma'aikatar revenue ta nan kano a branch enmu dake bomphai..." Ai BIGGY kam ji yayi kamar zai gangaro daga saman stairs en saboda dacen da yayi bak'aramin dad'i yajiba,dan dama ranar da UMMI tace ya kai mata takardunsa ya amsane kawai amma a ransa ya k'udurce shifa ba zai koma gidanba har sai bayan ya samu aiki wanda yayi k'ok'arin hakan a k'ashin kansa,wannan shi kad'ai zai sa su ganshi da k'ima.. Godiya yayiwa Allah,sannan ya kuma tabbatarwa da kansa lallai duk wanda yake laifi ya tuba ubangiji yana karb'an tubansa,kansa ya d'aga sama hawayen farin ciki suna sakko masa a hankali ya furta "Lallai ne ubangiji shi kad'ai yafi cancanta da a bautawa...Allah na gode maka da ka nufeni da tuba tun lokaci bai k'ureminba..." *~#TEAM KHUBRA.*~ *_#REAL SMASHER._* 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *22/ʝųlყ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *4⃣9⃣* *"A* lak'ar data had'amu da SAFWAN itace auratayya inda na auri k'anwarsa mai suna FALMATA" A nan ABBA'N KHUBRA ya dakata saboda wani tunanin daya bijiro masa wanda sam baiji dad'in hakanba,sai yanzu yake nadama da dana sanin abunda ya aikata,ciki kuwa harda saurin yanke hukunci,wanda Annabi (S.A.W) ya hanemu da mu yanke hukunci cikin fushi. LADIYO ya kalla da rinannun idanunsa da babu komai cikinsu face zallar b'acin rai wanda kana kallonsa zaka tabbatar had'e kuma da gano abunda ke k'unshe k'asan zuciyarsa. Muryarsa a shak'e ya kalli mutanen gurin ya kuma kallon LADIYO data sha jinin jikinta,sai da yayi gyaran murya sannan ya fara da fad'in "Da farko dai zan fara da yiwa wannan matsiyaciyar matar Allah ya isa,sannan kuma in shaida muku ina son ku zama shaida ni ABUBAKAR SA'ADU (MALAM BUBA) na saki LADIYO saki uku babu ni babu ita,daga yau ina son ta tattara kayanta tabarmun gidana na sallameta......" Innalillahi wa-inna ilaihi raji'un... Abunda mutanen gurin keta maimaitawa kenan kamar sa ari baki,ABBA'N KHALEEL ne ya fara magana "Haba MALAM ya zaka yanke irin wannan hukunci haka,bayan ka sani cewa ubangiji da kansa yana k'yamar saki irin wannan,sam bai dace kayi hukunci irin wannan ba koda kuwa wane irin laifi ta aikata maka,idan ka kyaleta da mahaliccinmu zai hukuntata komai girman laifinta kuwa..." Bai kai k'arsheba MALAMA BUBA ya dakatar da shi ta hanyar fad'in "Haba ALHAJI yanzu ita wannan matar da kake magana akanta kasan girman laifukanta kuwa?ko kuwa ni kasan meta aikatamin?kasan tsahon loacin data d'auka tana cutata?to ku saurareni yanzun zaku ji irin cutarwa da azabtarwar da wannan munafukar tayimin ni da iyalina...." *19 YEAR'S BACK......* "Shekaru sha tara 19 baya,na kasance malamin makarantar islamiyyane kamar yadda kuka ji suna na ABUBAKAR SA'ADU wanda akafi sani da MALAM BUBA,kaf garin nan idan ka tambaya tun daga kan manya da yara babu wanda bai sanniba saboda baiwa da Allah yayimin ta ilimin islama,ta wannan baiwar ne har na samu nake koyar da mutane da dama cikin garin nan namu,a lolacin ina da mata d'aya wacce itace LADIYO,muna zaune da ita lafiya tun bayan aurenmu wanda yake tun na saurayi da budurwa,tsahon rayuwar da mukayi da ita a wannan lokacin Allah baisa tana da rabon haihuwa ba,har muka kai kimanin shekaru goma Allah baisa ko da b'atan wata ta tab'a yiba,a kwana a tashi maganganu sunata yawo a gari kan matata bata tab'a haihuwaba,kai in tak'aice mukuma wasu har samuna suke sunamin magana kan idan na amince zasu bani auren k'annensu wasu suce y'ay'a ga mutanen da suka manyata kenan a wannan gari,gidanmu kuwa wajen mahaifana suma ba a kyale suba da wannan maganar,sai dai na basu hak'uri tare da godiya saboda karramawa da girmamani da sukayi wanda har ya jawo sunamin kyauta mai girma amma ni kuma ban karb'a ba,kwanci tashi asarar mai rai a shekara ta sha d'aya da aurenmu sai nayi wata tafiya zuwa garin DUTSE inda za a gudanar da wata *SEMINER* ta addini,cikin hukuncin Allah bayan zuwana garin duk yinin duniya idan muka gama abunda za muyi a gurin seminer sai mu fita don zaga gari.A wata ranar *LITININ* wacce bana jin zan iya mantawa da ita a iya tsahon rayuwata,kamar kullum mun fito muna zaga gari muka had'u da wata y'ar matashiyar budurwa kyakykyawa da ita,wacce ko ni idan aka bani abun zane ba lallaine na iya zana wacce ta kaitaba bare kuma wacce ta fita saboda kyau da Allah yayi mata sam bata da makusa ta kowane b'angare,nan dai maganganu iri-iri sukaita fitowa daga bakunan abokan tafiyata kan yaba kyau irin nata,jin abun da sukeyi yasa ni dai nayi shiru ban furta komaiba muka ci gaba da tafiya,wani ikon Allah yarinyar tana tafiya a gaba garemu mu kuma muna bayanta kusan duk hanyar data bi to ko muma ita muke bi daga dukkan alamu kuma aikenta akayi,mun biyo wata hanya ne kuma muka ga yarinyar na k'ok'arin shiga gida inda a nan wani mutum daya fara manyanta daga dukkan alamu kuma mahaifintane ya dakatar da ita,babban abun burgewa a tare da ita lokacin data tarar da shi a zaune tun daga nesa da shi kad'an ta cire takalmanta,sannan ta durk'usa ta gaida shi,bayan nan ta shige gida.. Tun daga wannan lokacin naji zuciyata ta kwad'aita da yanayin tarbiyya irin ta wannan baiwar Allah wacce ko sunanta ban saniba bare na tabbatar da nan ne gidansu ko a'a. Tun daga wannan ranar bamu sake biyo hanyar ba sai da muka kwana uku,sannan a yammaci na hud'u na shirya cikin shiga ta kamala kamar ko wane lokaci na d'auko hanya,ban zame ko inaba sai hanyar da muka gamu da wannan baiwar Allah,ina tafiya ina kuma duba gine-gine da yanayin unguwan har Allah yasa na kawo dai-dai wannan k'ofar gida data shiga,nan ko na samu guri na tsaya ina kuma k'arewa unguwar kallo,layin shiru babu mutane sosai zuwa wani lokaci sai wani yaro daga mak'otansu ya fito nan dai zuciyata ta rayamin na tambayi yaron ko Allah zaisa ya santa,banyi wani dogon tunaniba ko na kira yaron na tambayeshi ko yasan wata a gidan nan?,nan na siffanta masa ita da yanayuita,bud'ar bakin yaro ya furta eh yasanta sunanta *FALMATA* na masa dai y'an tambayoyi wanda bazasu gagara yaro ya amsaba ya bani amsa dai² da saninsa,sannan na zaro murtala na dank'a masa had'e da yi masa godiya,a guje yaron yabar gurin yana murna.Na jima tsaye a gurin kafin na bar unguwar.Tun daga wannan ranar ya zamemin d'abi'a kusan kullum saina je unguwar amma haka zan dawo ba tare da nayi magana da itaba. Bayan sati uku da faruwar wannan lamari ne kuma muka kammala abunda ya kaimu garin,nan muka shiga shirye-shiryen komawa gida,to kuma a cikin wannan lokacin ne na yanke shawaran tunkarar gidansu da magana ko nasamu nasara ko akasin haka,nan na shirya na ko kama hanyar gidansu,cikin sa'a ina zuwa unguwar tun daga nesa na hango wannan dattijo na ranar farko zaune a k'ofar gida,da sallama na tarar da shi bayan mun gaisa ban tsaya k'wauron bakiba nayi masa bayanin abunda ke tafe dani,nan dai yayi dariya shima mutumin sannan yayimin albishir d'in cewa shi ne mahaifinta,kuma yaji dad'in abunda nayi,sannan ya d'ora da fad'in zai samu yarinyar zasuyi magana idan har ta nuna ta amince to idan kuwa ta nuna akasin haka tofa sai dai nayi hak'uri dan shi kam ba zai mata doleba duk abunda take so shima shi yake so kuma shi zai bata,bayan nan yamin tambayoyi akan inda nake da sana'ata,ban b'oye komaiba na daga abunda ya shafeni na shaida masa,daga k'arshe kuma nayi masa sallama gami da godiya na kama hanyar komawa inda na fito. Kamar yadda yayimin alk'awarin bayan kwanaki na dawo dan jin yadda sukayi,kuwa na sake shiryawa daga garinmu dan a lokacin mun riga da mun koma gidajenmu,bayan naje mun gaisa da shi ya sanarmin da yadda sukayi,daga nan kuma ya shiga gidan da kansa ya kirawota,mun gaisa da ita bayan nan kuma tayi shiru saboda kunya da take da ko kallona bata iyayi a wannan lokaci,ban b'ata lokaciba na gabatar da kaina a gurinta a matsayin d'an takara na neman aurenta. In tak'aita muku labari haka soyayya gami da shak'uwa suka k'ullu a tsakaninmu da FALMATA,wanda ba'a d'auki lokaciba mahaifina kafin ya rasu sukaje nemamin auranta,kun dai san yadda ake sa rana a k'auye ba'a d'aukan lokaci kamar na birni su sukan sa lokaci tak'aitacce ne,sun yanke ranar aure watanni biyu masu zuwa,inda kowane b'angare aka shiga shiri,da farko LADIYO bata nuna damuwarta kan auren da zanyi ba ganin yadda mahaifiyata take sonta,bayan auren kuma sai wasu halayya na banza suka fara sako kai cikin al'amuranta wanda da gani kasan zuga ce take aiki a kanta. Muna zaune da FALMATA lafiya k'alau tun bayan aurenmu da ita da yake ita ba mai magana bace komai nata cikin sanyi take yinsa,wannan yasa ko da ake zugo LADIYO idan ta takaleta da fad'ama bata biye mata sai dai tayi shigewarta d'aki ta barta nan,haka itama zata k'araci masifar fad'anta ta bar gurin,ganin babu nasara sai ta canja salo inda a hankali ta soma jan FALMATA a jiki a gaban kowa tana nuna mata soyayya amma a zuciyarta babu wannan,ganin haka sai mutane suke sha'awar yadda suke zaune da juna,har wasuma suke fad'in ai MALAM BUBA yayi dacen mata na gari babu fad'a tsakaninsu. Kwanci tashi har muka shafe tsahon shekara aurena da FALMATA amma shiru babu wani labari ganin haka sai hankalin LADIYO ya dad'a kwanciya,ta sake sakankancewa babu su babu haihuwa tunda ga wata nanma na aura amma shiru itama babu labari,haka dai akaita tsegumi da gutsiri tsoma akan nine bana haihuwa,wani hukinci da iko sai ubangiji a cikin shekara ta biyu da aurenmu da FALMATA sai Allah ya azurtata da samun juna biyu wanda babu wani ko wata da ya ankara da hakan da yake babu wani laulayi da tayi,har cikinta ya kai kimanin wata shida,ita dai ajikinta taji chanji wanda mafi yawancin lokaci takan sanarmin amma sai nace mata kada ta damu babu komai,a lokacin data sake sanarmin tanajin abu na mata motsi a ciki sai nake fad'awa iya cewa ga abunda ta fad'a min,bud'ar bakin iya sai tacemin micijin ciki ke damunta,nan ta had'oni da jik'e-jik'en magunguna na gargajiya na kawo mata..." Nan MALAM BUBA ya dakata yana kallonsu da murmushi a fuskarsa sannan ya d'ora da fad'in "Kun san wani abun al'abi a cikin wannan labarin?" Babu wanda yayi magana cikinsu sai dai wasu cikinsu sun kad'a masa kai "To ku saurara kuji.....Abun da zai baku mamaki shi ne,har cikinta yakai wata tara babu wanda ya gane sai dai ita da kanta ta fuskanci akwai wani bak'on al'amari a tare da ita wanda ganin hakan kuma da tayi baisa ta sanar da kowaba, a lokacin ni kuma nakanje fatauci daga wannan gari zuwa wannan kuma nakan kwashi watanni uku-biyar ban waiwayo gida ba,to kunji dalili kenan daya sa babu wanda ya gane tana d'auke da juna biyu har tsahon lokacin... Masu iya magana kance "RANAR WANKA BA A B'OYON CIBI" k'warai kuwa haka yake wata ranar alhamis ciwo ya tasammata a cikin d'aki tun cikin dare addu'a kawai take saboda a lokacin bana gari,kuma gidan ya rage daga ita sai LADIYO wacce take nata d'akin daban itama,haka ciwon yake zuwa yana lafawa har dai Allah ya taimaka akayi asuba,a yanda take a haka ta lallab'a tayi sallar asuba,bayan nan kuma gari ya dad'a haske ciwo ya dad'a tadowa fiye da karon farko,tana wannan hali ne Allah ya kawo LADIYO shima zuwa tayi ta dubata ganin bata fitoba,samunta da tayi cikin ciwo wannan yasata hanzarin tafiya gidanmu ta kira mahaifiyata,ko kafin su k'araso gida har Allah ya sauketa lafiya,lokacin da suka shigo basuyi arba da komaiba sai da kukan jaririya nan suka k'arasa da sauri dan ganewa idanuwansu abunda suka ji gaskiyane ko kuwa,da zuwa suka tarar da ita a gefe tana maida numfashi jaririya a gefe tana tsala kuka babu b'ata lokaci iya ta gyarasu duka,tofa a lokacin ne kuma iya taimin aike kan lallai-lallai inzo gida tana son ganina a cikin kwanakin,lokacin da sak'onta ya riskeni banyi wata-wataba na shirya kayana sannan na kamo hanyar dawowa gida. Bayan dawowata na tarar da wannan abun farin ciki daya sameni,aikuwa nayi murna sosai da ganin wannan kyauta da ubangiji yamin,bayan kwanaki 7 yarinya taci sunan mahaifiyata *KHADIJATUL KHUBRA*,tun daga ranar da FALMATA ta haihu sai LADIYO ta dad'a taso da halayenta na farko ya zamana ko d'akin FALMATA ta daina zuwa,tun kuma ranar data haihu mahaifiyata ta dawo gidan d'akin FALMATA ta tare ta shiga bata kulawa da gyara ta musamman wannan dalilin yasa LADIYO kishi mai tsanani amma sai ta dinga dannewa bata nunawa a fili,sai daifa abunda ke zuciyarta kenan a duk lokacin data bud'e ido taga FALMATA da sabuwar jaririyar ji take kamar ta cinna musu wuta su k'one gaba d'aya kowama ya huta. Zuga kuwa da hud'uba kullum cikinsu take musamman idan ta fita tofa babu inda take zuwa sai gidan TABAWA,haka itama kullum cikin sintiri take a gidan nan,haka har suka k'ulla abunda suka k'ulla. Wata rana da asuba lokacin bayan iya ta koma gida KHUBRA nada watanni biyu a duniya,bayan mun idar da sallah a masallaci na kamo hanyan dawowa gida,abunda ya faru a wannan ranar idan na tuno ina jin b'acin rai da nadamar abunda na aikata a wannan lokacin,a ranar ba d'akin FALMATA nakeba bayan shigowata saina tuna ai ranar ban tashetaba da zan fita kasancewar ina sauri zani masallaci,tuna hakan da nayi yasa na nufi d'akinta da sauri kasancewar gari har yayi haske sosai,da zuwana d'akin abunda ya d'agamin hankali shine na tarar da ita kwance tasa KHUBRA a gaba,daga bayanta kuma wani k'ato ne jikinsa ko riga babu ya rungumeta suna bacci a haka,ganin wannan abu ya d'agamin hankali sosai ban tsaya jiraba na shiga jibgar k'aton ihunsa shi ya farkar da ita dama jaririyarmu,dukan daya isheshi yasa shi ficewa a guje,idanuna sun rufe da tsantsan b'acin rai nan babu jira na fice daga d'akin.Faruwar hakan babu jimawa na sake dawowa a lokacin har tayi sallah jikinta duk a sanyaye,tana rungume da y'arta tana bata abincinta,na shigo babu b'ata lokaci nace ta shirya zamuje gidansu,ita dai har lokacin batayi maganaba kuma jikiinta yayi mugun sanyi fiye da farko dana tarar da ita a d'akin mayafinta kawai ta d'auka ta goya KHUBRA a baya muka kama hanya ni da ita haka har muka isa gidansu,da zuwa nace ta shiga ciki idan BABA na nan tamin sallama da shi,ta shige ta barni nan a k'ofar gida. Bayan fitowar BABA muka gaisa a mutunce sannan na shiga koro masa bayanin abunda ya faru,shi dai yayi shiru yana saurarona har na k'are labari,sannan ya kalleni da mamaki shimfid'e a saman fuskarsa ya shiga fad'in "Nayi mamaki daka zomin da wannan rikitaccen labarin naka mai kama da k'anzon kurege,kuma tabbas kaima ka bani mamaki da wani yazomin da wannan maganar wallahi da sai nayi k'ararsa amma da yake kaine mun barka da Allah,amma zan tambayeka wani abu game da y'ata,shin lokacin da kazo neman aurenta ka tarar da ita tana tara samari ne ko kuwa? sannan bayan ka aureta ka sameta a cikakkiyar budurwa ko a'a? tana da kamun kai ko a'a a bayan aurenku?" Duka amsoshin d'aya ne A'a,tabbas ba haka halayenta suke ba,amma a lokacin da yake abunka sa sharrin zuciya sai nake ganin kamar fa ta aikata,nan na k'ek'asa k'asa na kuma dube shi nace "Nifa BABA duka nasan ba haka bane amma na sani ko ta sauya hali ne bayan nan" Sosai maganata ta b'ata masa rai amma sai ya danne ya ce "To yanzu daka dawo da ita kuma me yake faruwa? Nan ko na furta "Na dawo muku da ita ne,sannan kuma tunda Allah yasa haka halinta yake na saketa saki d'aya idan ta samu miji tayi aure..." Ba sakin ne ya b'ata masa raiba illa cin mutuncin da nayi musu na saida na kawota har gida sannan kuma nace na saketa a gaban idonsa,nan ya ce "To BUBA munji abunda ya faru mun kuma gode amma ka jirani na fito maka da y'arka,kamar yadda ka dawomin da tawa y'ar nima ina son tabbatar maka da bazan rik'e maka taka y'arba,saboda haka saika nema mata wata uwar" Yana gama fad'in haka ya shiga gida ya fito hannunsa d'auke da jaririyar,nan ya mik'omin ita nako sa hannu na karb'a na mik'e zan tafi,maimakon na tafi sai na bud'e bakina na kuma kalli tsabar idonsa nace "Kamar yadda ka bani y'ata in sha Allah zan rik'eta da yardar Allah kuma babu abunda zai samemu,kamar yadda zan tafi da ita yanzu to ko ku tabbatar na tafi da ita kenan bazaku sake ganintaba haka nima na tafi kenan ni da ku har abada...." Ina gama fad'a masa ban jira ya sake maganaba nayi gaba abuna.. "Tun daga wannan rana rainonta ya dawo hannun IYA mahaifiyata saboda LADIYO ko kallo bata isheta ba,KHUBRA nada wata uku a duniya mahaifina ya rasu daga nan ne kuma IYA ta dawo gidanmu da zama a d'akin da FALMATA ta zauna,tana kuma ci gaba da kula da ita. Kimanin watanni biyu da rasuwar mahaifina,IYA ta fara rashin lafiya a lokacin annoba ce ta shigo garin nan na amai da gudawa wanda kwanaki biyar da fara jinyar tata itama tace ga garinku nan,a wannan lokacin naji mutuwar nan da akamin a tsakanin watanni biyar na samu k'aruwa na samun y'a na kuma rasa mahaifana biyu.. Da farko na damu sosai bayan mutuwar IYA amma daga baya sai na dangana na koma ga Allah,sannan naci gaba da kula da KHUBRA duk wani abu da uwa za tayi mata ni nake mata shi dan LADIYO dai-dai da sau d'aya bata tab'a d'aukanta ba saboda tsanar da tayi mata. Lokacin da bakinta ya fara bud'ewa na shiga koyar da ita karatun addini,a haka muka ci gaba da rayuwa duk inda zani ina tare da ita,bacci ma tare mukeyi a haka har Allah yasa ta fara wayo sosai ta fara gane wasu abubuwa. Rana ta farko datamin wata magana na shiga damuwa amma sai dai na dake a lokacin data ke tambayeta ina UMMA'NTA? amsa d'aya na bata kamar yadda nayi alk'awarin bazan kaita gurin mahaifiyartaba shi ne nace mata ta mutu tun bayan data haifeta,ranar data ji haka yini tayi kamar mara lafiya,daga baya kuma ta ware kamar sauran lokaci. Lokacin data k'ara girma shekarunta sun kai ta fara aikace-aikace gudun kada a zageni da kuma k'ananan maganganu dake tasowa yasa na fara barinta a gida sannan muka daina kwana tare,a lokacin ne kuma aikin gidan nan ya dawo kanta komai ita keyi tun bata iyaba har ta gama k'warewa,idan zani d'ibo ruwa ita ke karb'a ta tafi ta hanani zuwa,ina kallo tana wahala amma sam idan nayi magana sai ta nunamin babu komai.. Haka muka dunga rayuwa da dad'i babu cikin hukuncin Allah,har kuma ta zama budurwa,wanda nanma kyau irin nata data gado a wajen mahaifiyarta dan kam babu abunda ta bari na mahaifiyarta yasa hassada ta sake kunno kai ta b'angaren wannan dai shaid'aniya inda bata kyalemuba har sai da tayi nasarar rabamu..." Nan ya kuma kwashe abunda ya faru tun daga barin KHUBRA a gidan har zuwa yau da suka zo ya sanar da su... Al-ajabi kam sunyi shi,tasbihi kawai suke suna kuma jinjina abun,kan KHUBRA na cinyan ABBA'NTA banda kuka babu abunda take jin labarin mahaifiyarta da abunda ya faru,Allah ya isa kam LADIYO ta shata koma ince tana kan sha a gurin KHUBRA da sauran mutanen gurin musamman BB da ZUHRA da suke ganin kamar su hakan ya faru da su,kowa a zuciyarsa yake fad'in albarkacin bakinsa da kuma irin hukuncin da zai yanke mata saboda su a ganinsu hukuncin da ABBA ya yanke matama yayi kad'an... Muryan ABBA'N KHUBRA tasa su maida hankulansu kanshi inda yaci gaba da fad'in "Bayan faruwar wannan abun ne kuma wata rana ina zaune akayi sallama dani dana fita sai naga mutum tsaye ganin ban sanshiba na daure muka gaisa,sannan nace masa ban shaida shiba,shi ne ya kwashemin komai ya sanar dani,dama shi ne wanda na kama tare da matata,jin haka raina ya sake b'aci sosai amma sai ya shiga bani hak'uri sannan ya sanarmin shima sashi akayi kuma ba kowa ya turo shi ba sai LADIYO da taimakon k'awarta TABAWA,nan ya nemi gafarata na yafe masa sannan na sanar masa yaje ya nemi yafiyar wacce ya aikatawa laifin,na masa kwatancen gidansu saboda ni kam a lokacin bazan iya zuwa gidanba saboda a ganina da wane ido zan kalli wannan baiwar Allah ita da mahaifinta nace ina neman yafiyarsu? to kuma ana haka ne bayan wannan mutumin ya tafi,na shigo gida kwana biyu tsakani nayi MUGUN GAMO........" Labarin mugun kamun da yayiwa LADIYO da wannan k'asurgumin tsohon banzan ya basu,nan kowa ya shiga fito da abunda ke bakinsa suna fad'in "Sakayya ce Allah ya nuna mata,Allah ya wadaran hali irin wannan.." LADIYO dai tana gefe babu baki sai ido tayi k'us da ita kanta a k'asa saboda kunya data lullub'eta ji take inama k'asar gurin ta bud'e ta shige,da tasan abunda zai biyo baya kenan da bata zaunaba,da tasan ta felle k'afafunta tun lokacin da MALAM BUBA'N ya saketa amma yanzun kam inaa lokaci ya k'ure mata... *SOME MINUTE'S LEFT......* Bayan wucewar wasu mintuna,an gama jimami da alhini,ABBA'N KHALEEL yake shaida ma ABBA'N KHUBRA cewa "Ya kamata ka daure kaje gidansu domin neman yafiyar abunda ya wuce saboda idan babu rayuwa akwai mutuwa..." "In sha Allah zanje na nemi gafarar BABA dama ita kanta FALMATAN..............." 😱😱😱😱😱😱😱. *Huhhh!!! kunji fa fan's abunda ABBA'N KHUBRA yace kenan bai san MAMA'N KHUBRA ta jima da rasuwa bama ko me yake nufi???* *~#TEAM KHUBRA.~* *_#®EAL $MASHER._* 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *22/ʝųlყ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ 5⃣0⃣ *B* ayan k'ura ta lafa komai kuma ya dai-daita an gama jimamin abubuwa da suka gabata sannan kuma an shaidawa ABBA'N KHUBRA labarin yadda ta rayu a gurinsu a matsayin y'ar aiki da kuma matsayinta yanzun a gurinsu,daga nan kuma suka gangara kan mak'asudin zancen daya kawosu garin. Sosai yayi farin cikin abunda suka sanar masa,daga nan ya shaida ma ABBA'N BB cewa "Duk abunda kaga ya dace ka aikata SAFWAN ba sai ka neme niba idan ya so daga baya naji hukuncin daka yanke,saboda KHUBRA y'arka ce kuma bayan haka kuma kuna da hak'k'i akanta a matsayinku na iyayenta kuma dangin mahaifiyarta..." Wannan karramawa da ABBA'N KHUBRA yayi masa yaji dad'inta,take kuwa shima ya yanke nasa hukuncin inda yace "To Alhamdulillah! da Allah yasa al'amura suka kasance haka,gaskiya nafi kowa farin cikin faruwar hakan,amma magana biyu gareni zan fad'a yanzun kuma ba ga kowa ba sai kai MALAM BUBA" Nan suka sake maida hankali gurin ABBA don jin me kuma zai fad'a "Ina ganin a yanzu tunda abubuwa da dama sun faru zan nemi wata alfarma a gurinka..." ABBA'N KHUBRA ya kalleshi yana murmushi yace "Fad'i duk abunda kake so ni kuma in sha Allah idan baifi k'arfina ba zanyi maka" Murmushin shima ABBA yayi sannan yace "Ai nasan baifiba ma,amma dai bari mu gani.......Ba komai zan fad'a ba dama illa ina so nace maka.....tunda Allah yasa yanzun baka da kowa a garin nan mai zai hana bazaka bimu mu koma can birni tare ba,kaga kaima zakafi samun kwanciyar hankali ace kana ganin y'arka a kowane lokaci,behind ma kuma yanzun ba iyali gareka ba,sannan banajin a garin nan kana da wani d'an uwa ko kuwa me kuke gani...?" "K'warai wannan maganar da kayi nima Allah ne yasa ban yitaba amma nima hangena kenan" ABBA'N KHALEEL ya fad'a yana murmushi Ga ABBA'N KHUBRA kuwa yaso musawa buk'atar tasu ganin yadda suka jajirce yasa shi amincewa.. Kowa ka kalli fuskarsa cikin mutanen gurin babu komai samanta face farin ciki da annashuwa. Bayan wucewar wani lokaci komai ya lafa an kuma gama yanke shawara game da hukunci,shirin tafiya ya kankama in da ABBA ya kammala had'a kayansa aka sasu a mota,gaba d'aya sun mik'e da niyyar kama hanyan komawa inda suka fito.. Suna shirin fita ZUHRA ta kalli ABBA tana fad'in "ABBA ai kunyi mantuwa..." Duka suka juya suna kallonta da neman k'arin bayanin mantuwar da sukayi LADIYO ta nuna musu dake cikin rumfa sai kallonsu take da fuskar munafukai musammanma KHUBRA data koma kamar baturiya dan kyau data k'ara,sai lokacin LADIYO ke nadama game da dana sanin bata aikata abunda tayiba duba da yadda KHUBRA'N ta koma,lokaci guda ta bayyanar mata a matsayin y'ar dangi mai cikakken asali,komawa tayi wata kalar tausayi ganin irin kallon da mutanen gurin ke mata. A fusace ABBA'N KHUBRA yayo kanta yana fad'in "Bak'ar munafuka al-gunguma kinzo kin ficemin a gida ko kuwa saina raunataki" Wani ice ya rarumo faskare guda ya dumfarota da shi,da sauri ABBA'N BB ya rik'e shi yana murmushi had'e da girgiza masa kai "Haba MALAM BUBA me zai kaika aikata abunda ko a baya baka aikataba,kana so ne ka k'arasa gawar da ba taka bane?...." Da sauri kuma ya tsaya harara ya aika mata sannan ya jefeta da icen,aiko nan ta juya da niyyar guduwa d'aki icen ya sauka a tsakiyar bayanta ji kake timmm,wani ihu ta kurma su ko su ZUHRA,ASHNA,FATAHIYYA me za suyi inba dariyaba,tsabar mugunta harda rik'e ciki,BB ya kallesu yana fad'in "Dillah ku rufawa mutane baki,ko meye abun dariya a nan kuma ohooo...." Kyal-kyalewa KHUBRA tayi da dariya dan ita sai a lokacin da yayi magana tata dariyar tazo,nan ta shiga dariya saboda mugunta irinta KHUBRA baya ga hawaye harda durk'usawa a k'asa tasa hannu ta dafe gefen cikinta.. Kallonta yayi yana dad'a d'aure fuska,lallaima yarinyar nan ta raina shi,banda iskanci shi zai musu magana ta tsaya tana masa dariya,lallai ko zata bawa mutanen garinsu labari idan suka had'u.. Lower lip nasa ya cije yana kallonta k'asa-k'asa fuskar nan a had'e kamar bai tab'a dariyaba,ZUHRA data kalli yanayinsa da sauri ta dunguri KHUBRA tana nuna mata BB,d'an bakinta ta murgud'a k'asa-k'asa tayi magana "Ina ruwana to da shi....." Abunda KHUBRA bata saniba tsaf BB yaga abunda sukayi kuma yaji maganar da tayi,kwafa yayi had'e da girgiza kansa.. "Kinzo kin fice ko kuwa sai na danganaki da gaban mai gari?..." "Wollahi MALAM ban san ina zaniba bani da kowa sai MA'U ita kuma ban san ina takeba a fad'in duniyar nan,dan Allah ka rufamin asiri dan sonka da manzon rahama kada ka koreni,idan ka koreni ina zani.....?" "Ke dallah dakata ina ruwana da inda zaki?? ni yanzu bani da alak'a ta kusa ko ta nesa dake,tun wuri kuma ki zo ki fice kafin na fusata jikinki ya kuma gaya miki ina fatan kinji dai abunda na fad'a miki....." Kuka wiiwii take tana bashi hak'uri amma bai biya ta kantaba,nan suka fice daga gidan,haka LADIYO ta k'ullo y'an kayanta ta fito tana kallo MALAM ya sawa gidan pad lock ya rufe gidan,sannan suka d'au hanyan komawa.... Maimakon su d'auki hanyan KANO sai gani suka yi BB dake driving ya yanke hanya,cikin garin DUTSE ya nufa,babu wanda yayi magana cikin iyayen da suke zaune,a tunaninsu a kwai abunda zaiyi a garin,basu tsinci kansu a ko inaba sai k'ofar gidan KAKA,parking yayi sannan suka fita gaba d'aya da masu son tambaya duk sun yi shiru,jikin ABBA'N BB da kuma ABBA'N KHUBRA duk yayi sanyi saboda su kam ko daga mafarki suka tashi aka kawo su nan sun gane ko ina ne,su kuma y'an matan babu wacce tayi tunanin wani abu game da gidan da suka zo. BB da KHALEEL na gaba,basu tsaya shawara ba suka shiga gidan su KHUBRA na bayansu har cikin gidan,su ABBA na waje suna shawaran yadda zasu fuskanci KAKA dan dukansu masu laifi ne a gare shi,har basu sanma y'ay'an nasu sun shigeba. Da sallama suka shiga kamar zuwansu na farko haka tsakar gidan yake cike da mutane sunata aikace-aikacensu game da hirarraki irin na mutanen k'auye,bayan sun gaisa da matan gidan kai tsaye suka nufi turakar KAKA dan sun san kam yana nan kamar yadda take a wancan lokacin,da shigarsu cikin turakar suka tarar da KAKA na karatun AL-QUR'AN saboda hadda gare shi,sai da ya kai aya sannan ya amsa musu sallama'n da sukayi,nan BB da tsokana yace "Sadak'allahul-aziiym tsoho mai ran k'arfe,ashe a kwai tsohuwar hadda bata guduba..." Dariya KAKA yayi sannan yace "Yo an fad'a muku haddar da mukayi irin taku ce ta yanzu,mu gwagwarmayar da mukayi ai ko rabi baza kuyiba....Idan kuma ka musa to mu gwada mu gani waye zai nasara..." Gaba d'aya suka sa dariya har y'an matan sannan suka gaisa,kallon y'an matan yayi yana murmushi kafin yayi magana su ABBA suka shigo da yake ABBA'NSU BB ne a gaba hakan yasa KAKA baiga na can bayaba,kallon ABBA yayi yana murmushi sannan ya fara magana "Idonka kenan ko SAFWAN..." Sunkuyar da kai ABBA yayi k'asa ba tare da yayi maganaba "Kayi hak'uri BABA ka kuma yafemin dan Allah,komai daya faru nima ba a son raina ya faruba...." "Ai shi kenan Allah ya yafe mana baki d'aya...." Gaisuwa ta musamman akayi ga kaka,nan KAKA ya sake kallon BB yana fad'in "ABOKINA wad'annan y'an matan kumafa ?" Dariya BB yayi dan yasan da shi yake "Baka sansuba ko...?" "To banda abunka da na sansu zan tambaya ne.....?" Gabatar masa da su yayi a matsayin jikokinsa da bai saniba sai yanzun.... Dariya KAKA yana kallonsu duka,ABBA ya kalleshi yaga yana kallon KHUBRA,d'an murmushi yayi yace "BABA ka santa ne....?" "Gidanku SAFWAN ni kuma na zama abun tsokana ne kam a gurinka?" "A'a BABA naga kana kallonta ne kamar ka santa..." 'Dan murmushi ABBA yayi sannan ya kalli KHUBRA dake murmushi ya kuma kalli KAKA yace "To tunda ka santa fad'i wace ce....?" Bud'ar bakin KAKA yace "Yo wannan kam duk wanda ya kalleta ya ganka ai yasan y'arka ce ba sai an tambayaba....kuma har mene abun wahala anan da zaku sani gaba kai da d'anka daga zuwanku,ce muku akai bazan ganeba ne...?" Dariya suka sa mishi saboda paul daya buga gurin fad'in ko wace ce "Haba BABA ka dai sake kallonta sosai dawa take maka kama" Sake kallonta BABA yayi sannan ya kalli ABBA yace "Nifa bana son shegantaka yo to dawa take kama idan ba da kaiba...." Sai da suka gama wana shi sannan ABBA yayi gyaran murya,duka suka juya suna kallonsa "BABA dan Allah duk abunda zaka ji a yanzu ina so ka maida shi ba komaiba,kayi hak'uri ka yafewa wad'anda suka maka laifi,nasan kasani sai dai tunatarwa dan Allah BABA..." Murmushi KAKA yayi masa ba tare da yayi maganaba,kallon KAKA ABBA yayi sannan ya kalli KHUBRA a hankali yace "BABA wannan da kake gani tabbas y'ata ce amma bani na haifeta ba.....jikarka ce ta wajen y'arka FALMATA....." KAKA dake kwance idan zai tashi sai an taimaka masa jin an ambaci FALMATA bai san lokacin daya mik'e zauneba da kansa. "Ka ce me SAFWAN...? Shin kam yaushe na fara wasa da kai kamar haka?..." "BABA sam cikin maganar da nayi babu wasa a ciki,jikarka ce y'ar wajen FALMATA..." Kallonta KAKA yake tabbas ga kammani nan,sai dai kuma abunda yasa yace y'ar SAFWAN ence kaf gidan kuma kaf cikin y'ay'ansa su biyu suke kama da juna,ko wasu tagwayen da ake haifarsu identical baza su nuna musu kamaba.. Hawaye KAKA ya shiga yi na tausayinta yana mik'awa KHUBRA'N hannu,da rarrafe ta isa kusa da shi sosai ya rik'eta ita ko data samu abunda take so nan ta kwantar da kanta kan laps en KAKA feeling so happier take jinta saboda kasancewarta y'ar dangi kuma gata tare da su.Kanta KAKA yake shafawa lokacin daya goge fuskarsa,nan kuma aka shiga maida zancen abunda ya faru baya,sai a lokacin KAKA ya hango ABBA'N KHUBRA dake zaune da tun shigowarsu kansa na k'asa sai yanzun daya d'ago KAKA ya kula da shi.. "Idonka kenan kaima ko ABUBAKAR?...Shi kenan kuma tun daga waccan ranar baka sake dawowaba...na sani dukanmu munyi ba dai-daiba daga mu har kai,kuma sai daga baya muka gane kuskuren da muka aikatawa yarinyar da bata jiba bata ganiba,tabbas dukanmu munyi laifi kuma sai Allah ya saka mata hak'k'inta da muka d'auka....ki gafarta mana JIKATA....." Yanayin da KAKA yayi magana shi yasa jikin ABBA yin sanyi duka sai yaji ya muzanta a gabansa,nan ya shiga neman yafiyarsa.... Bayan nan kuma ABBA ya tambayi KAKA shin ko FALMATA tana nan ko kuwa wani auren ta sake yi.. Sai da KAKA ya matse idanunsa sannan ya shiga basu labarin tun daga ranar da ABBA ya dawo da ita gida da kuma irin yadda suka yi gwagwarmaya gurin karb'ar KHUBRA da yayi ya kaiwa mahaifinta,a lokacin da yake cikin fushi...sannan ya d'ora da fad'in "To tun daga wannan ranar ne kuma ta shiga damuwa saboda abunda na aikata akan y'arta d'aya tal,daga lokacin ta sakama kanta damuwa sosai wacce a k'arshe duk bamu fargaba,sai da ciwo yaci k'arfinta bayan shekaru data shafe tana tare da ciwon har ciwo yaci ya cinye jikinta,yau kimanin shekaru bakwai (7) kenan da rasuwarta...Sai dai kafin rasuwarta ta bar min wasiyyar ko da zaka zo wani lokacin in sanar maka cewar ta yafe maka abunda kayi mata,kuma itama tana neman ka yafe mata." Kowa dake cikin parlor'n sai da yaji mutuwar MAMA'N KHUBRA,tare kuma da nema mata yafiyar mahalicci... An yafewa juna an kuma maida abunda ya wuce ya riga ya wuce,sannan an rungumi juna,dangi ya dad'a had'uwa bayan d'umbin lokaci da aka d'auka a tarwatse,tsintsiyar data tarwatse ta koma cikin mad'aurinta.... Sai yamma lokacin duka gida an had'u kowa nata murna da farin cikin ganin d'an uwansa,KAKA ya sake gabatar da su a matsayin y'ay'a da jikokinsa da ba kowa ya sansuba... ABBA'N KHALEEL ne ya matsala kusa da KAKA nan ya sanar da shi dalilin zuwansu garin,na neman auren KHUBRA da KHALEEL yake son yi,sosai gidan kowa yayi murna da jin hakan,bayan an gama magana aka dank'a alhakin yanke ranar auren ga KAKA a matsayinsa na SHUGABA,yaji dad'i sosai bai yi wata-wataba ko ya dank'ara yanke lokaci nan da makonni takwas wanda yayi dai-dai da watanni biyu kenan masu zuwa.....Nanfa murna ta dad's k'aruwa fiye data farko. BB kam jin wannan maganar da kuma hunkuci na KAKA ba k'aramin tada masa da hankali yayi ba,da k'yar yayi ta maza ya danne damuwarsa a lokacin,har aka gama duk maganar da za a yi kansa na k'asa dai-dai da sau d'aya baiyi kuskuren d'agowaba bare wani ya fuskanci yanayin da yake ciki.. Wajejen Maghreeb sukayi sallama da kowa kan zasu koma,bakin KHALEEL kam sam yak'i rufuwa saboda farin cikin da yake ciki a yau,bayan sunma mutanen gidan sallama kan zasu koma amma zasu dawo bada jimawaba,har bakin mota su OLD KHALEED suka rakosu sai da sukaga barinsu a line en sannan suna koma gida cike da murna da far in cikin al-amarin d'aya wakana a wannan rana. KHALEEL ne ya amshi driving tunda a zuwa BB ne ya kawosu garin,godiya BB yayiwa Allah daya sa ba shi zaiyi driving ba,dan yana da tabbacin idan shi ne to babu makawa kam k'arshe sai dai su tsinci kansu a jirkice gefen k'walta......... Tafiyar yau ta zama tarihi a garesu gaba d'aya family'n kowa na farin cikin yadda tafiyar ta kasance idan aka cire BB da wani gefe na zuciyarsa babu komai cikinsa face tsantsar k'unci,idanunsa da take jin sun masa nauyi ya rufe kamar mai bacci duk wani yanayinsa KHALEEL yana kula da shi,shi kam sababbin halayen da aminin nasa ya bijiro da su a kwanakin suna bashi mamaki matuk'a,shiko BB gani yake hakan da yayi shi yafi masa,a gurinsa kam cewa yayi wannan itace MAFITA a tare da shi.... *TAMBAYOYI......* _Game da littafin *Y'AR GARUWA*.._ 1-Shin a cikin wannan littafi wane ne jarumi & jarumar ku?? 2-Wane mutum ne yafi burgeka/burgeki?? 3-Wane mutum ka/kika fi tsana a ciki??? 4-Wane mutane kukafi so a cikin wannan littafin??? 5-Mene ne kuskuren mabuciyar a cikin labarin nata?? 6-Shin yaya matsayin wannan littafi yake a gurinku??? 7-Idan akace ka/ki bawa wannan littafi mark,mark nawa kuke ganin zai karb'a daga gurinku?? 8-Shin kuna son wannan littafin ko kuwa?? _Sai munji daga gareku......_ *Comment for more page's....* 💃💃💃 *~#TEAM KHUBRA.~* *_#®EAL $MASHER._* 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *23/ʝųlყ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~__________________________~* _Naga comments enku kuma naji dad'in hakan sosaifa,sai dai k'orafinku gareni akan *MAMA'N KHUBRA* mafi yawancinku amsarku iri d'aya ce *"BAI KAMATA NACE TA MUTUBA"* sai dai abu d'aya nake son tunasar damu shi ne,itafa mutuwa wajibice akan ko wane bawa,walau ka shirya ko baka shiryaba,tabbas idan lokacinka yayi dole ne ka amsa kiran mahalicci,kuma wannan novel en da kuke gani ba wai zance muku true life story bane,just na k'irk'ire shi ne amma kumin afuwa tunda haka ya faru,dama tun farko haka na tsara labarin so ina ganin ba abun damuwa bane dan an rasa mutum d'aya a cikin labarin,sannan hakan shi ne solution ga MAMA'N KHUBRA dama su kansu ahalinta coz koda ace tana raye tofa kada ku manta abunda aka mata k'azafinsa ba zai tab'a gogewa ba,kunsan k'azafi a kwai ciwo sosai,so ina neman afuwanku..._ _Fatan Allah yasa muyi kyakyawan k'arshe....Ameen._ *Really luv u fan's..* ♥ *~__________________________~* *DON ALLAH INA ROK'ONKU DA KU DUBI GIRMAN ALLAH DA YANAYIN YADDA NAYI MAGANA DA MANYAN BAK'AK'E,DAN ALLAH KUYI HAK'URI DA YA'DA JITA-JITA AKAN WAI ANYI KIDNAPPING SIS ENA,SISINA TANA NAN CIKIN K'OSHIN LAFIYA KUMA BABU ABUNDA YA SAMETA CIKIN HUKUNCIN ALLAH TANA NAN SAIMA K'ARIN LAFIYA DA KWANCIYAR HANKALI DA TAKE DA'DA SAMU FIYE DA BAYA,MASU YI DAN ALLAH KUYI HAK'URI HAKANAN,DAN BAMU SAN DAME ZAMU JIBA DA SAK'ONNINKU KO KUWA DA CIWON MAGANAR KIDNAPPE EN,INA FATAN ZAKU FUSKANCI NUFINA...MUN GODE.* _Stay wealthy *CWEET SIS HABIBA IDREES (HUBBEEY)* nd now i turn ur name into *INDO K'AFAR.........* 😉💔 *~__________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ 5⃣1⃣ *S* ai misalin k'arfe 10:00pm suka iso gida,a gida'n UMMI suka fara yin branch inda ABBA'N KHALEEL da KHALEEL suka fara sauka,bayan sun musu sallama kuma BB ya amshi driving,ikon Allah kad'ai ya kaisu gida,yana yin parking bai tsaya jiran fitansu ba ya fice a motan ya nufi cikin gidan. Yanayin yadda yake tafiya kad'ai ya isa yasa a gane akwai matsala a tattare da shi,saboda yadda yake tafiya a durk'ushe dafe da side en k'irjinsa na hagu. Da yake kowa a gajiye ya dawo saboda zaman motan da suka d'iba coz tafiyan yini guda akwai wahala,babu wanda ya lura da yanayinsa kowa ya shige nasa gefen. ABBA kad'ai aka bari tare da ABBA'N KHUBRA,shima bayan daya nuna masa gefen da zai zauna sukayi sallama ya wuce shima. Gidan shiru daga dukkan alamu mutanen gidan sun jima da yin bacci,hakan ce kuwa ta kasance dan wasu kam a lokacinma basu san inda kawunansu sukeba. HAJIYA MURJA na d'aki ta kishingid'a,tana nan ta jiyo shigowansu gidan da motsinsu amma sai bata yi yunk'urin fitaba,har zuwa lokacin da ABBA ya shigo,nan ne tayi masa barka da dawowa,da mamaki ya kalleta yana fad'in "A'a dama bakiyi bacci bane madam?...da naji gidan shiru haka nayi tsammanin ko har kunyi bacci nema..." 'Dan murmushi tayi kafin ta bashi amsa "Uhmmmm! ta yaya zan iya bacci yanzun bayan ban san a wane hali yarana suka kasanceba..." Teasingly ya kalleta da salon tsokana fal saman fuskarsa lokacin yana shirin zama kusa da k'afafunta "Ke dai fad'amin gaskiya y'ay'anki kikafi damuwa da su ko kuwa mijinki....? Baki bud'e take kallonsa "Wane irin kuma miji y'ay'an dai...." Dariya sosai maganarta tasa shi wanda ganin yanayin yadda yake yasa ita da kanta itama sai data dara "Tohh! tunda kince haka let's see the truth....." "Wane irin gaskiya kuma kake buk'atar gani a wannan maganar....?" Winking yayi mata "Ahhhh! ya wuce na nemi wani d'akin na kwana,tunda ni ba a buk'ar sanin nawa damuwan..." Cikin sauri ta katse shi "Aaaaa! nifa ba haka nake nufiba,kawai dai nace haka ne saboda kaga su yara ne ba wani girma garesuba,bayan haka ma kuma basu tab'a tafiya dogo kamar hakaba...." Duk maganar da takeyi tana yi ne da kanta a langab'e kamar wata yarinya,koda yake za a iya ce mata yarinya,ammafa a gurin mijinta. Cike da nishad'i suna tsokanar juna suka kwanta,bacci mai cike da kwanciyar hankali kam wannan family sun same shi,musamman b'angaren ABBA'N BB,ABBA'N KHUBRA,KHALEEL,dama sauran tawagar tafiya except one person. A b'angaren BB kuwa tun daya samu ya shige bed room nasa,yayima Allah godiya kan bed ya zube zuciyarsa kamar zata faso chest ensa ta fito,duk lokacin daya tuna abunda ya faru a yau sai yaji zuciyarsa na masa k'aik'ayi ji yake inama bai san KHUBRA da KHALEEL ba a tsahon rayuwarsa da ya fi masa alkhairi sama da wannan al'amarin daya faru.. Da k'yar ya samu bacci ya d'auke shi shima sai gabanin salla'n asubah,bacci yake amma duk wanda ya kalleshi zai iya gano babu komai cikin baccin nasa face zallan wahala.... 《《》》 Tun daga ranar da BIGGY ya yankama yaransa warning dai-dai da sau d'aya babu wanda ya kuma kuskuren yi masa shaye-shaye,tun daga ranan suka shiga hankalinsu,saboda tun kafin wannan lokacin suka san halinsa bare kuma yanzun da suke ganin ya canja wasu sabbin halaye dan yanzun ba kamar da bane.. Ranar Mondy kamar yadda aka buk'aci yaje *REVENUE OFFICE* en,aiko ya shirya da takardunsa a envelope ya fice,bai jira d'aukan motaba don a cewarsa idan suka ganshi a mota da matsala danko yana da tabbacin ba zasu tab'a bashi offer en aikinba.Babban dalili kenan da yasa BIGGY yake faman yawo a NAPEP. Cikin hukuncin Allah aka masa interview ya kuma samu nasara inda suka mik'a shi b'angaren accountant da yake fannin *ECONOMICS* ya karanta,kuma babu laifi result ensa yayi kyau. Aiki yake ka'in da na'in,babu damuwar komai a tare dashi hakane yasa shi bayan samun wannan nutsuwar da gyara halayensa da yayi ya yanke shawaran ziyartar danginsa,bayan zuwansu garin nasu ya tarar da baffaninsa na cikin matsananciyar buk'ata da rashi,taimako ya basu wanda su da kansu sai da wasu cikinsu suka zubarda hawaye saboda suka banzatar da rayuwarsa a bayan rasuwar mahaifansa wanda gini ya zubowa lokacin da suke tsaka da bacci,daga lokacin kuma da rik'onsa ya koma hannun kishiyar mama'nsa wacce ta azabtar da dashi na tsayin wani lokaci bai sake samun kulawa daga gurin dangin mahaifin nasa ba bare ya san muhimmancin su gare shi,wahalar yau daban ta gobe daban har ta kai da tana sa shi y'an sace-sace da haurawa gidajen mutane yana kwasowa yana kawo mata,ganin babu abunda take bashi ko da ya sato mata goal ne kuwa shima daga bisani ya gudu coz ko abinci ta girka rabonsa a ciki k'anzo ne,babba'n dalili kenan daya sashi guduwa don neman na kansa kuma ya tsaya da k'afafunsa ta hanyar ci gaba da wannan sana'a,wanda a lokacin daya baro k'auyen nasu ya kammala makarantar primary har ya shiga k'aramar secondary,bayan dawowarsa birnin kano'n dabo kuma bai zauna hakaba sai da yayi duk wani k'ok'ari da zaiyi ya maida kansa makaranta babban gata kenan da BIGGY yayiwa kansa a rayuwarsa ta baya. Yasha sa albarka gurin dangi da suka guje shi abaya,wanda kafin ya dawo bakin aikinsa sai daya sanarwa baffanin nasa buk'atarsa ta zuwa nema masa aure cikin wani sati,babu musu bare jan lokaci duka suka amsawa buk'atarsa tare da yi masa alk'awarin zuwansu cikin weekend,ba don komaiba kuwa sai dan ganin yanzun yana cikin rufin asiri sannan kuma shi zasu mora ba shi zai moresu ba.. _Duniya kenan...._ 《《》》 A safiyar ranar ta lahadi gaba gidan basu iya tashi da wuriba kasancewar akwai gajiyar tafiya tattare da su wannan dalili yasa gidan yake shiru,misalin k'arfe 10:00am suka fara fitowa d'aya bayan d'aya.ZUHRA data riga su tashi ta nufi d'akunan baccin nasu tana tashinsu,gurin KHUBRA ta dawo data bari a bed room coz su tare suke kwana suke tashi tun bayan bayyanarta komai nasu tare suke yinsa. "Yawwa CWEETY ki tashi kinga yanzun ABBA yace yana son ganinmu duka a parlor.." Juyi tayi tana bud'e idanunta da suka mata nauyi coz baccin bawai ya isheta bane,da kyar ta tashi ta shirya,a parlor ta tarar da su sun hallara suna shirin yin break fast. Kusa da ZUHRA ta zauna ABBA ta fara gaisarwa sannan MAMA,sai kuma sauran y'an uwanta data tambaya lafiyarsu da yadda suka tashi. Fuskokinsu babu alamun damuwa suke break,ABBA ya kalli yaran gaba d'aya cikin so da kulawa "Ina BB ne kam...? Gaba d'aya kowa yana nan banda shi ko baccin ne bai sake shiba har yanzun...?" Dariya sukayi duka gurin "ABBA kaima ka koma ce masa BB ne?" ZUHRA tayi tambayan tana dariya dan tasan ABBA da tsokana ya fad'i hakan "Aaaaa! to nima ba dole na koma fad'in haka ba,nima ai naga BB ena ne ko....?" Yayi tambayan yana kallon MAMA da take dariyan drama'n nasu "To ai ABBA baka san me yasa muke fad'an hakaba...." Kallonta yayi yana murmushi "Ku rik'e dalilinku nima na rik'e nawa....Kuma dai duk da haka nima da BB zan kira shi ko kuna so ko baku so.." All family en they were happy da wannan moment's da suka tsinci kawunansu aciki,MAMA ma ba a barta a bayaba dan ABBA ya sanar da ita komai game da matsayin KHUBRA a gurinsa,sai yanzun idan ta kalleta take jin kunyar abubuwan da suka aikata mata ita da su ASHNA lallai ta dad'a tabbatarwa da ubangiji baya bacci kuma duk wanda ka zalunta yana gaggawa tare da saukar maka da naka isharar,ta kuma dad'a godewa Allah daya sa KHUBRA'N ta bayyana ba tare da wani yaci zarafinta ba,da ace wani abu ya sameta to tabbas bata san kuma da wane ido zata kalli ABBA ba saboda gungun laifuka da ta aikata,ita kam wannanma kad'ai ya isheta hujja da zata kafa idan taga wani mai irin halinta.Har yau kuma tana dad'a neman afuwar Ubangiji kan laifuffukanta. Bayan sun gama break aka koma hira,suna tsaka da hira KHALEEL yayi sallama,ZUHRA ce ta dunguri KHUBRA cikin rad'a take mata magana "CWEETY ga oga nan ya zo ina fatan zaki bashi kulawa ta musamman" Uwar harara KHUBRA ta maka mata,d'an bakinta ta dad'a tsukewa tana kallonta k'asa-k'asa ta furta "Bafa nason iskanci kin sani..." "Dillah wane iskanci,madam idan zaki zage ki bashi kulawa to idan kuma ba hakaba to y'an matan zamani sayi miki k'afa d'aya...." Still tayi tana kallon ZUHRA da bakinta a bud'e "Heeyyy! beb ki rufe bakin kada flies su cike miki shi..." "Uhmm! Allah ya baki lafiya dan naga kina buk'atan addu'ah..." Aiko ZUHRA ta amsa da ameen tana mata gwalo,bata sake kulata ba duk yadda taita tsokanarta,ganin tak'i biye mata yasa ta mik'e ta nufi bed room enta,cikin closet enta ta bud'e tana duba wani gown nata da take mutuwar so,a jikinsa leda en ta fad'o,da sauri ta tsuguna tana d'auko ledan tunanin inda ta same shi take,can kuma ta tuna yadda akayi ta mallakeshi ita sam ma ta manta da shi sai yanzun data gani ta tuna da tsawon lokacin daya d'auka a ajiye,d'an bud'ewa tayi tana fiddo kwalin ciki phone ne sabo mai maituk'ar kyau,zaroshi tayi duka tana dad'a dubawa,daga bayansa wani farin paper ya fad'o da mamaki ta d'auka ganin kamar letter ne ciki nan ta shiga ware shi a hankali kuma ta shiga bin kalmomin dake rubuce *DEAR CWEET SIS.* _"Am so sorry lil sis! nasan hukuncin dana yanke baza kiji dad'in saba sai dai babu yadda zanyi hakan ya zamemin dole,ba komai yasa na rubuta miki wannan short note enba sai kan wani dalili nawa......na yanke hukuncin tafiya don barin k'asar saboda samun nutsuwar zuciya ba don komaiba sai dan soyayya da take neman salwantar da ruhina....sai dai kash na makaro saboda wadda nakeyi dominta bata sanma ina yiba,behind kuma wani ya rigani,ina rok'onki daki tayani da addu'ah sannan kuma kada ki bawa kowa labarin abunda ya faru duk da nasan a lokacin da zaki samu wannan sak'on nayi nisa da ku......ga phone nan ko da wani abun ya faru a gida zamu dinga magana dake,idan na sauka a inda naje zan nemeki,ina muku fatan alkhairi...na barku lafiya.._ _Ur's BB..._ Ai ZUHRA na idar da karatun wasik'ar hankali tashe ta fice daga d'akin bata zame ko inaba sai hanyan bedroom ensa tana rafka masa kira,har ta shiga bata dena kiransaba,kaf d'akin ta kalla babu kowa ciki hankalinta a mugun tashe ta zube a gurin tana sakin kuka.. "Me yasa BB zakamana haka....ko mai yayi farko ai yana da k'arshe,ni kam bazan tab'a bari ka rasa farin cikin kaba,indai har akan soyayya zaka tafi ka barmu na tabbata wannan abun yafi komai muhimmanci a tare da kai....." Kuka sosai take ta kife fuskanta da hannayenta biyu,dafa ta akayi ta baya a d'an tsorace ta d'ago tana kallonsa ganinsa gabanta yasa tayi saurin goge fuskarta paper en ta mik'a masa,karb'a yayi yana dubawa,bayan ya gama dubawa kafin tayi magana sai gani tayi kawai ya d'aga paper ya yagashi,sai da yayi masa gutsi-gutsi sannan ya rabu da shi.. "BB me yasa.......?" Da sauri ya dakatar da ita,ta hanyar d'aga mata hannu alamar tayi shiru,shirun kuwa tayi itama tana binsa da kallon mamaki,tafiya ya soma yi har ya isa bakin bed ensa ya zauna,tana kula da yanayin yadda yake tafiya da gani kasan dauriya ne kawai yake yi,da tausayawa take fidda wasu sabbin hawayen cikin kuka ta fara masa magana "YAYANAH! me yasa bazaka fad'i abunda ke damunkaba ka b'oye mana, shin baka tunanin akan ko zamu iya nema maka mafita...kana ganin hukuncin da kayi yayi kenan?please dan Allah kayi magana kaga ina jin tsoron kada wani ciwon ya kamaka please.....!" Murmushin k'arfin hali yayi "Noo! CWEET SIS babu abunda ke damuna yanzun kam wancan letterma k'arya ne a da ne yanzun kam babu wanda nake so ko yake sona,wancan lokacin ne kawai kuma kema ki kwantar da hankalinki dan wacce nake so en tuni har iyayenta sun mata aure kinga ko bashi da amfani na fad'a,abunda kawai nake so dake ki tayani addu'ah Allah ya yayemin abunda ke damuna...." Sosai ta gama yarda da maganar daya fad'a cikin wani yanayi na tsananin tausayi take kallonsa idanunta suna dad'a kawo ruwa "Shi kenan BBNAH amma sam ban so akace haka ya faru da kaiba na so ace ka samu ABINDA RANKA KE SO (SAWWAMATEEY),Allah ya maka canji mafi alkhairi....amma! Amma ai ka fasa tafiyan ko?" A fili ya amsa da ameen ya kuma tabbatar mata d'aya fasa tuni,a zuciyansa ko fad'i yake "Lallai yaro yarone yanzun ta yarda da abunda na fad'a kenan" "Amma YAYANAH meya sameka kake tafiya ahaka da alama wani abu kuma na damunkafa...me yasa baka je kaga DR ba kake zaune da rashin lafiya?" Tambayan nata ya zo masa a bazata shi yasa sai da ya d'auki wasu minutes kafin ya iya bata amsa "Sorry CWEETY na bige ne a toilet yanzun shi yasa kikaga haka" "Eyyahhh! sannu YAYANAH nayi tunanin ko wani abun ke damunka daban shi yasa na damu...." "Noo! babu komai kam ki kwantar da hankalinki yanzunma idan na gama abunda nake yi zanje naga DR ko da wani matsalan da ban wanda ban san da shiba.." "Yawwa YAYANAH barin je to sai ka dawo Allah ya kiyaye hanya" Kallon tausayi yabita da shi har ta fice karo na farko kenan da yayi mata k'arya shi kam sam ya rasa dalilinma daya sa yayi mata hakan sai kuma yanzun yake jin haushin kansa da faruwar hakan.Har ya kammala shiryawa ya fito still tafiyan shi bai koma normal ba,duk wanda ya kalleshi zai gane hakan a tare da shi,kaf sai da suka kalleshi ganin yadda yake tafiya a duk'e kamar wani tsohon daya shekara d'ari.d'an dakatawa yayi ya gaida ABBA da MAMA,daga bisani kuma ya mik'awa KHALEEL hannu fuska babu yabo bare fallasa,sauran kuma suka gaida shi,amsawanma da kyar yake yi,ya kama hanyan ficewa daga parlor Maganar ABBA ta dakatar da shi wanda yasa shi dole ya juyo ya kalleshi fuska a dame "SON me yake damunka kake tafiya haka....?" Kafin ya bashi amsa ZUHRA data b'illo daga corridor tace "ABBA bigewa yayi a toilet yanzun nima muka gama magana da shi..." "Eyyahhh! Allah ya kiyaye....To amma ina zaka je kuma kana irin wannan tafiyan?" "ABBA hospital fa yacemin zashi yaga DR ko da akwai wani abun daban da yake damunsa ko...?" "Ehh to hakanma yayi Allah ya kiyaye gaba" Da ameen suka amsa duka nan BB ya sauke ajiyan zuciya mai nauyi saboda shi da kansa yasan Allah ne ya taimakeshi da ZUHRA tazo at the right time kuma tayi saving ensa a hannun ABBA da bai san me zai biyo baya ba,side en da take zaune ya kalla sun wani had'e kai da ZUHRA suna matsa phone,a hankali ya juya da niyyan ficewa daga parlor'n again KHALEEL ya sake dakatar da shi ta hanyar fad'in "Lemme help u MAN,muje tare hospital en" Ganin yadda idanu suka masa yawa yasa bai k'i amsan tayin KHALEEL enba amma kam da niyyansa yace bai so sai dai ya mazeee suka fita tare inda KHALEEL yake driving ensu har sukaje hospital suka dawo,sai dai duk k'ok'arin KHALEEL na sanin matsalan aminin nasa hakan bai faruba dan BB ya hana DR fad'an matsalan a gaban KHALEEL kawai ya ce masa ya bashi maganin da yake ganin shine zai masa maganin rashin lafiyansa,after kuma suka kamo hanyan dawowa duk motsinsa yana kula da shi kam sam bai yadda da abunda ZUHRA ta fad'a yana damun KHALEED enba kawai dai yayi shiru ne,ko da suka dawo gida BB ya kalli KHALEEL tare da fad'in "Thnks!..." Daga haka ya fice bai kuma magana yayi bedroom a nan ya duba prescriptions en nasa,aiko nan ya tsorata da ganinsu..... 《《》》 Kwanaki suna ta dad'a wucewa inda ya zama a lokacin har family en BIGGY sunzo sun kuma gana da iyayen BEAUTY'NSA a take babu b'ata lokaci 3ple ABBA suka tsaida rana dai² da bikin KHALEEL da KHUBRA wanda KAKA ya tsaida da kansa... Musamman BB ya d'auki hanya bayan dawowansu daga DUTSE inda ya koma don ganin jikinsa da kuma maganan kaishi a duba lafiyan k'afan nasa,tunda yajema da BAFFA'N nasa da maganar ya kalleshi da fuskar damuwa yake fad'in "Kayya dai takwara nan da kake ganinmu babu maganin da bamu kawo masa ba amma yak'i amfani da shi,shi nan BABA da kake gani magani ko wane iri ne ba sonsa yakeba,shi yasama kaga mun zuba idanu muma tunda babu yadda za muyi..." "To amma BAFFA kam ai wannan ciwon nasa bana a zuba masa ido bane...ko kuwa bai damu da lafiyar k'afafun nasa bane?" "Ehhh to nima dai abunda na kasa ganowa kenan,da yake ku y'an zamani ne la'alla idan kayi masa wani dabaran ma samu ya amshi maganin a wannan lokacin,amma muma kanmu ciwon nasa na damunmu kawai dai babu yadda za muyine kuma yak'i yarda akaishi asibiti a duba k'afar..." "Shi kenan in sha Allah komai zai zo da sauk'i,bari na masa sallama a yau nake son komawa kuma gashi yamma ya kawo jiki..." Koda suka koma gurin KAKA sallama kad'ai yayi masa sannan ya kamo hanyan dawowa gida,tun daga lokacin ya k'udire niyyan nemo masa magani daga na asibiti har zuwa na gargajiya dan bai san da wanne za a daceba saboda masu iya magana kan ce "idan dama yak'i to sai a koma hagu" Neman magani yayita yi bayan dawowarsa sai daya tabbatar ya samu magungunan daya aminta dasu sannan ya kama hanyan komawa garin,da taimakon Allah ko bayan gumurzu da suka sha da KAKA ya amince ya karb'i prescriptions en dan kafewa yayi akan magungunan suna kisa shi ko haka kawai bai shirya mutuwa yanzuba..... _Kunjifa KAKUS da gigin tsufa...._ Lokaci baya jira sai dai a jira shi,haka yake inji masu iya magana kuma su kan ce "duk abunda kaga bai zoba to tabbas ba a sa masa lokaciba" k'warai kuwa dan ko idan har ansa masa lokaci sai ya zo kuma harma ya wuce. Biki nata dad'a matsowa ko wane gefe suna shiri babu ji bare gani,zuwa wannan lokaci duk wanda yaga ASHNA da BIGGY sai ya so sake kallonsu saboda soyayya,shak'uwa gami kuma da yarda da juna dake tsakaninsu,b'angaren su KHALEEL kuwa ba a cewa komai saboda sanin su nasu tsarin ba irin na kowa bane abun dai sai wanda ya gani,biki na k'aratowa amare da angwaye hidimomi sai dad'a shan kawunansu suke haka lokacin yaci gaba da kusantowa.......... *COMMENT FOR MORE PAGE'S......* 💃💃💃 *~#TEAM KHUBRA.~* *_®єαl $mαѕhєr._* 😉 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *24/ʝųlყ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ 5⃣2⃣ *Y* au gaba d'aya abunda yayi saura a kwanakin da suka rage musu baifi kwanaki goma ѕhα hud'u ba,duka gidan ya dad'a hautsinewa,kowa ka gani ba shida lokacin zama aikace-aikace da hidima duk sun sasu gaba,hatta da su kansu amaren ba wani lokacin zama garesu ba,yau suna nan gobe can. Cikin mota suke tafe sai surutu suke su uku KHUBRA,ZUHRA sai kuma ASHNA,shi kansa KHALEEL da yake driving hiran nasu har hawan masa kai yake saboda yawon da suka sha yau gashi duk ya gaji,ba shida burin daya wuce su isa gida ko Allah zaisa ya samu nutsuwa. Daf da sallan isha suka iso gida,yana ajiyesu ko bai tsaya hiraba yayi musu sallama gami da juyawa,su kansu da yake a gajiye suke da shigansu gida,basu tsaya ko inaba sai d'aki,a kan bed ZUHRA ta zube tana fad'in "Wash! wallahi duk joints d'ina ciwo sukemin haka wannan yawon raba I.V en yake....tabbb wallahi idan na tashi aure bazan iya wannan wahalarba,gara mutanen kada su zo." ASHNA dake zaune kusa da ita ta kalleta tana fad'in "Lallai yarinya ce ke,ta ina zaki wani sakowa mutane zancen aurenki bayan samarinma koransu kike,kenan wai gaki malama to waima ni da wane suna zanna kiranki ustaziya ko me....?" "Ke kika sani kuma wannan,ni rabani da SAMARIN BANA (ASY KHALEEL) ba komai a cikinsu sai k'arya kamar ragowar yak'i....Fatan dai Allah ya zab'a mana mafi alkhairi.." "Wollahi kin gama magana tunda kika nemi zab'in mafi alkhairi,da sannu zaki ganshi wollah...." KHUBRA ce tayi maganar dan duk hiran da suke bata sa bakiba sai lokacin,saboda lokacin da suka shigo tana k'ok'arin cire kayanta,shirin shiga wanka ta gama nan ko tayi hanyan toilet.. Mintuna k'alilan ta fito jikinta jik'e gada ita sai towel iya cinyanta,sai k'arami data d'aure kanta ta gaba ya bada shape na harafin V. "Ha'aaa! ya kuma naji kunyi shiru ko har kun gama hiran ne?" Ta tambaya tana coge k'afa d'aya,ASHNA dake faman chart ta juyo tana kallonta "Uhmm! nikam abunda nake yafi min wannan firan da kike magana" Dariya tayi dan tasan me take nufi,batayi maganaba ta wuce tana fad'in "To ai sai ku tashi kuyi wankan dan ni ina gama abunda nake kwanciya zanyi.....wallahi dana shiga wankan nanma kamar kada na fito saboda dad'in ruwan da naji...." "Kina iya komawa ai in yaso sai muyi using wani toilet en.." Hankalinta na kan waya tana chat take bada amsa,da sauri ko ASHNA ta kalleta ehfa tunda ke baza kiyi wankanba ai kya fad'i haka dubi irin gajiyar da muka kwaso amma nice haka,bari kiga ke idan kin gama chart en kyayi nan da talatainin dare" Wayan ta ajiye tana shirin core kayanta,kafin tayi yunk'urin mik'ewa ai har ZUHRA ta dire a guje ta shige toilet en,baki ASHNA ta saki KHUBRA ko me za tayi mata ba dariyaba,tana cikin dariyan aka bud'e k'ofan hankalinsu duka ya tafi kan k'ofa suna son ganin waye haka babu knocking ya danno musu kai.. FATAHIYYA ta shigo tana fad'in "BRIDE AUNTIES.....Ashe kun dawo amma ko ku nemeni..shi ne kuka gudo nan kuna hira babu ni..." "Allah sarki k'anwarmu yi hak'uri kinji shigowanmu kenan muma.." "Kai AUNTY KHUBRA shigowa'nkufa kenan kika ce bayan gashi nan har wanka kikayi kinga kenan kun jima da dawowa...Shi kenan ai tunda kuna nuna min triberlism dama ni nasan ba wani damuwa kukayi da niba....wa ya sanima ko idan kunyi aure zaku neme ni..." Fuskanta a shagwab'e tayi maganar cike da nuna damuwa "Yi hak'uri kinji....me zaisa mu kuwa bazamu nemeki ba,k'arewa ma ni dake tare zamu tafi kinji..." KHUBRA tayi maganar tana rik'e hannunta.. "Su tafiya tare manya,ai ga hanya nan zaku iya abunda yafi hakama...Amma ko dai angon a ranar zai ce ku koma inda kuka fito.." Yanayin da tayi maganar yasa su darawa dukansu,dai² lokacin kuma wayan dake saman mirror ta hau ruri,kallon gurin KHUBRA tayi had'e da tab'e baki,banza tayi suka ci gaba da hiransu har kiran ya katse,zuwa can aka sake kira nanma wayan sai ring yake "Haba sis kina jifa ana kiranki kuma kin share kamar ba ke ake kiraba..." ASHNA tayi magana cike da tuhuma kuma take kallon KHUBRA'N da tayi kunnen uwar shegu kamar bada ita take ba.Ganin bata da niyyan motsawa yasa ita ASHNA'R nufan gurin da wayan yake ta d'auka tana duba mai kiran,YAH KHALEEL ta gani a rubuce saman phone en sai lilo sunan yake "Ungo ni YAH KHALEEL ke kirankima ashe kika wani share kamar bake ba,nifa wannan gulmar ne banso idan zaki amsa ki amsa,mata tana so sai wani kaucewa kike...Allah yasa ayi ai auren nan naga yadda zaki yi..Ni wallahi har so nake naga yadda zaki koma idan anyin auren..Zaki ci gaba da yi masa duhun kai ne ko kuwa ya za ayi nema ohoon muku..." Ita dai KHUBRA shiru tayi mata bata tankaba sai wayan data karb'a ta ajiye gefenta ba tare da tayi tunanin d'aukaba,saima hira da take k'ok'arin sako musu. FATAHIYYA ta kalleta lokacin da kira na uku ya shigo wayan nata "AUNTY da kin d'auka kinji me zai ce miki...Kinga yanzun kada kisa shi tunanin ko wani abu ya faru..." "Ke kyale shi ai yasan a gajiye nake ni kuma yanzun baran iya d'aukaba.....Dan yanzun yana ganin na amsa zai tsare ni da surutu ni kuma gaskiya bacci nake ji...." "Aifa shi yasa naga kinyi baccin yanzun..kina nan kin wani yi gwaraf a gaban k'anwa zaku dasa surutu shi ne harda wani cewa bacci kike ji....Allah dai yana kallonki kuma sai dai ki tunasar da wani wulak'anci babu kyau.." Ita dai FATAHIYYA tana kallonsu idan wannan yayi magana ta juya ta kalle shi idan wannan ya amsa sai ta sake juyawa,rashin d'aukan wayan da KHUBRA tayi yasa FATAHIYYA d'auka a hankali ta furta "Hello! YAH KHALEEL ina wuni....?" "A'a FATAHIYYA ya kike...? Ina AUNTY'NKI fa?" "Lahh! YAH KHALEEL damafa gani nayi kana kira ita kuma tana shigowa tayi bacci.." "Ok! to shi kenan na gode k'anwata,da safe mayi magana da ita dama kiranta nayi naji lafiyanta,amma tunda tayi bacci shi kenan kada ki tasheta,na gode sosai.." Sallama sukayi ta ajiye wayan,sai lokacin hankalin KHUBRA ya kwanta saboda tunda ta d'auki wayan hankalinta bai kwantaba sai da taji sunyi sallama kuma duk abunda suka fad'a taji tunda wayan a handsfree ta sata. Ajiyan heart tayi ASHNA kam shiru tayi musu amma lamarin na KHUBRA na bata mamaki musamman da auren ya dad'a gabatowa.. Bata kuma kulasuba har suka gama abunda za suyi k'arshe kuma kowacce ta kwanta.Ita dai tana kan waya suna chart da nata prince en kuma tana cikin garin ciki........ *ONE WEEK TO MARRIAGE....* A gurguje ya fito daga mota ya nufi cikin gida dan dama a kwai abunda ya shigo dashi yanzun da yake ta sauri kada wani ya tsaida shi. Karo suka yi da sauri ya d'ago dan ganin me ya faru haka,kallonta ya tsaya yi ganinta yake kamar cikin mafarkin daya saba a y'an kwanakin da auren nan ya matso,sam baya son abunda zai had'a shi da ita bare ya kawowa ransa wani tunanin ko yasa damuwanta a ranshi,sai daifa hakan da yake ba k'aramin azabtuwa yakeba,duba da yadda rashin ganin nata ya dad'a jefa shi cikin wani hali,ganin da ya mata a yanzunma duk da a rashin sani hakan ya faru,sosai ta dad'a yi masa kyau musamman da bai gantaba cikin y'an kwanakin da suka wuce,kamar an dasa su zuciyarsa sai sak'a masa abubuwa da dama take a kanta,cikin sauri ya d'auke kansa tare kuma da ci gaba da tafiya abunsa.. Kallonsa kawai tayi ta tab'e baki sannan ta juya tana tafiya abunta zuciyarta na fad'in "Anya ko YAH ba wani abu ke damunsa ba?...Ko kuwa dai ni kad'ai nake ganin haka?....To amma idan har ba gizoba naga ya rame sosai ba kamar yanda na sanshiba...." Da sauri kuma ta d'age kafad'a tana fad'in "Kai to ni ina ruwana ma da damuwa'rsa....Shi ya sani ko wani abu na damunsa...Can ta matse masa ni banda damuwa...Allah yayi mutum sai d'an karen nunk'ufurci..." Hanyan guarding ta nufa tana shiga ta nemi guri ta zauna,bata jima ba a gurin ko ZUHRA ta shigo gurin "Ki ce nan kika yo yau kuma nan kika tuno bayan da kin daina zuwa" "Ehh fa na gaji da zama cikin d'aki ne kawai shi yasa na yanke shawaran zuwa nan nasha iska.... "Wallahi dai kam nima haka nan nake jin zuwa nan yau shi yasa na fito ban kuma yi tunanin kina nanba..." Suna cikin hiran motan KHALEEL ta kunno kai da sauri KHUBRA ta kwanta a k'asa saman grasses en tana rufe ido,dan ita kam bata son surutun KHALEEL a yanzun sam bata shiryawa jinsu ba,a nan ya tarar dasu shima ko ya zauna,mafi yawanci hiran tsakanin KHALEEL da ZUHRA ne dan dama ita ce abokiyar kuma y'ar rakiyar zance duk lokacin da yazo hira.Ita kam KHUBRA ko magana yayi mata amsanta tsaf sai mutum ya k'irga su saboda yadda take magana a tak'aice.. Labari suke sai dariya suke duka ta window ya hangosu su uku a cikin lambun,da yake lambun yafi kusa da window ensa shi yasa yake iya jiyo sautin dariyarsu. Yanayinsu gwanin sha'awa haka nan yau kuma yaji yana sha'awar fita zuwa gurinsu ko ya rage damuwan dake ransa. Suit en dake jikinsa ya zare ya sauya kayan dake jikinsa zuwa masu sauk'i sannan ya fice zuwa gurinsu dan a lokaci ji yayi ba zai iya fitanba.Tun kafin ya k'araso fuskarsa a sake ba kamar kwanakin da suka wuceba ya iskesu,ganin fuskarsa a sake wanda shi kansa KHALEEL ganin canji a tare da shi sai da yayi mamaki abu d'aya ya hana shi nuna hakan murnan da yake na ganin aminin nasa ya sakko yasashi jan bakinsa ya tsuke ko a fuska kuma bai nuna masa komaiba,hira sosai da suka jima basuyi ba suke wanda k'arshe suka gangaro kan maganar program's da za ayi a bikin,lokacin da KHALEEL yayi maganar sai da BB yaji wani iri kan maganar dinner da yayi,kawai dai ya danne ne,zuciyarsa na masa k'una,maganar KHUBRA ta katse masa tunani wanda har sai da ya d'ago ya kalleta "Ni kam dan Allah wai dole ne sai anyi wad'annan bidi'o'in..." Kallonta sukayi su duka suna mamaki "To banda abunki CWEETY ai hakan shi zai nunawa duniya irin farin da muke ciki..." Tab'e baki tayi tana fad'in "Tabbb ni kam wallahi da da yadda zanyi da nayi dan kawai na hana wannan abun....Dan ni kam har ga Allah ba so nakeba" "Saboda me zaki ce haka CWEETY...? Sai data kalleta sannan tace "Saboda bana son hayaniya ne kawai shi yasa,na tabbata lokacin zanyi ta fama da ciwon kai" KHALEEL kam sam bai so hakan ba amma saboda jin abunda ta fad'a yasa yace "To ai ina ganin hakan ba abun damuwa bane,abu ne da za ayi na k'aramin lokaci kuma ba dad'ewa za ayi ana yiba,so ina ganin babu wani abu da zai faru in sha Allah...." BB kam bai ce komai ba game da muhawaran da suke saima waya daya ci gaba da dannawa kamar baya gurin,hiran ya koma tsakanin ZUHRA da KHALEEL dan ita ta maye matsayin BB na babban aboki da za ayi shawaran da shi itama amarya tana gefe tayi musu shiru kamar bata gurin...... Tun da suka shiga satin komai ya dad'a kachamewa musamman da kwanaki kad'ai ya rage musu a fara biki. A lokacin duk wanda ya kalli KHUBRA babu lallai ya shaidata saboda kyau data k'ara akan nata,fita ko a cikin satin babu mai yinta tsakaninsu kullum suna d'aki daga su sai halinsu MAMA kad'ai ke da ikon ganinsu sai ko mai gyan jiki dake zuwa kullum tana gyaresu wanda gaba d'ayan su akewa sai dai na amaren yafi na sauran,a haka sauran kwanaki suka soma cimmusu. Kamar yadda yake a tsare bayan kamu da walima ta mata zallah da za'a gudanar a shagulgulan bikin,sai d'aurin aure wanda daga shi sai dinner da za ayi bayan nan kuma za a wuce da amare gidajensu. Duk wannan budirin da ake har lokacin BB baiyi kuskuren d'aukan invitation card enba bare ya gayyaci wani aboki ko wani mutum mai muhimmanci a rayuwarsa nasama da aka bashi tunda ya amsa ya bud'e closet ensa ya cillasu,tun daga ranar ko bai sake bi ta kansuba,hasalima duk lokacin da KHALEEL zai kirashi akan zaizo suje rabon card en sai dai ya bashi excuse akan aiki ya rik'e shi office,duk naci da magiya babu irin wanda KHALEEL bai masaba amma sam yak'i rakashi,kan dole ya hak'ura ba dan ya soba sai dan babu yadda zaiyi da shi. Tun daga ranar da sukayi haka da shi ko ta k'arshe bai sake nemansa daya raka shinba sai dai duk inda zashi ya kama hanyansa shi d'aya,wasu daga cikin abokansu ko har tsiya suke masa idan sun ganshi shi kad'ai,sai dai ya fake musu da BB aiki ya tsare shi a office amma sun san babu yadda za ayi su ganshi shi kad'ai... Haka har ranakun biki suka fara shigowa.... Kamar yadda aka shirya haka aka soma gudanar da events en ba tare da k'arya ko nuna su wasu bane,duk k'in KHUBRA na rashin son shiga taron jama'a abun ya gagara,kan dole take aiwatar da komai ba dan ranta na soba,duk inda ta juya jama'a ne daga ko wane sashi.A hankali saboda hayaniya da k'aran kayan kid'an wajen suka soma damunta nan ko ciwon kai yace bisimillah... Duk yadda take ji ajikinta d'auriya kad'ai take amma sam tak'i nunawa mutane hakan. *23/SEPTEMBER,2018.* Rana bata k'arya akace sai dai uwar d'iya taji kunya,a yau ne dubban jama'a suka taru a babban masallacin na *UMAR BIN KATTAB* dake *ZARIA ROAD* dan shaida d'aurin auren,d'aurin aure mai cike da tarihi.. Shiga ta alfarma na hango manyan mutanen uku wanda duk ya gansu a wannan lokaci tabbas sai ya san sun bayyana a gurin,manyan ALHAZAWA da a wannan lokaci tarihinsu da labarinsu ya baza birni da k'auye cikin lokaci k'alilan,wanda dama dayawa daga cikin mutane sun san da su a wancan zamanin na baya sai a wannan lokaci labarinsu yafi yin shura... Fuskokinsu kad'ai mutum zai kalla ya shaida tsantsan farin ciki dake shimfid'e samansu,jama'a sai gaisawa suke da su suna musu fata da kuma sanyawar alkhairi. Da misalin k'arfe 10:30am KHALEEL na hango cikin shiga wacce take bayyana eh lallaifa wannan young man en akwai wani abu dake faruwa. Kallo d'aya tak ya isa mutum ya gane hasken dake tare da shi a ranar wanda a dai² lokacin ya juya yana kallon BB daya koma kamar ba shiba,shigansu iri d'aya komai dake sanye jikin d'aya tabbas idan ka kalli d'aya zaka ganta ba aikin kowa bane sai BB dan shi yayi iya yinsa na ganin ta faru,kallon juna suka yi,sannan suka yima juna murmushi kafin suka fice a tare,BB ke driven inda ango KHALEEL ke gefensa "Wai MAN lafiyarka k'alau kuwa...." Kallonsa yayi ta cikin bak'in glass dake fuskarsa kafiin nan kuma ya furta "Me ka gani kuma...?" "Yo to kai d'in ne ai kake bani mamaki...cikin lokaci k'alilan kamar wani mai shafar jinnu..yau a ganka kana d'aci gobe kuma ka sake rikid'ewa ka koma ba kaiba" Dariya yayi "To waya sani ne ko na koma cin wahainiya...kasan idan mutum na ci rikid'ewa yake yau ka ganshi a wannan siffar gobe kuma ya sake komawa wata" Kallonsa kawai KHALEEL yayi ya furta "Allah ya kyauta..." "Ameen...!" "To amma shi wannan glass enfa daka toshe da shi kamar wani sabon makaho,na lafiya ne kuwa?" Banza ya masa yayi kamar bazai yi maganaba,can kuma kamar wanda aka tilasta ya furta "Idan baka son ganinsa ba dole aka maka sai ka kalle niba ai...Duk ka wani dami mutane da surutu dama kasan daka tashi karatu ka zama *JOURNALIST* dan naga yanzun abunda kafi k'auna kenan...Mutum sai d'an karen surutu kamar ya had'iya farrot,Allah yasa kada ka koyawa k'anwata wannan zancen..." Dariya sosai maganar da yadda BB yake da face ensa ya bashi,KHALEEL jinsa yake yafi kowa dace a wannan ranar saboda aminin nasa ya dad'a sakin jiki da shi dan yau kam gashi harda su tsokana,suna ta faman tsokanan juna suka isa masallacin inda ake jiran k'arasowarsu..... *11:00am* Aka fara addu'ah sannan bayan gubatar da siga da akayi a cikin massalacin wanda duk abunda ake BB na wajen masallaci yak'i shiga sai KHALEEL en kawai ya shiga,aka fara sanar da d'aurin auren inda mai sanarwar ya fara sanarwar da d'aurin auren ta cikin abun magana kamar haka... _AN 'DAURA AUREN *IBRAHIM-KHALEEL* DA AMARYARSA *KHADIJATUL-KHUBRA* AKAN SADAKI NAIRA NA GUGAN NAIRA HAR NAIRA DUBU 'DARI BIYAR........_ Ai jin wannan sanarwa take idanun BB dake cikin glass suka soma kawo ruwa,a lokacin kam ya gama tabbatarwa da kansa ya masifar yiwa kansa,ya cuci kansa cutar da baya tsammanin akwai wata cuta da zaiwa kansa kamarta,yasan yayi k'auron baki inda yanzu gashi nan abunda ya jawowa kansa.....Ya tabbata kam yanzun hak'uri ya zame masa dole. Gefen k'irjinsa ya dafe saboda yadda yaji yana masa zafi lokaci guda tsaiwa ta soma neman ta gagare shi,a daddafe ya nufi mota shi kad'ai yasan me yake ji a guje kuma ya fizgi motan tare da bar in gurin..............😱😱😱😱 _Wayyoooo Allah ínα masoya KHALEED (BB) ku kαwσ αgαjí kαdα wani abu ya same shi........_ _mσvє fσwαrd tσ thє nєхt pαgє..._ *COMMENT FOR MORE PAGE'S* *~#TEAM KHUBRA-KHALEEL.~* *_®єαl $mαѕhєr._* 😉 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/ *©® 2018* *25/ʝųlყ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* _rígíjí gαвjí....wαní kαчα ѕαí αmαlє...mαí kαmαr zuwα kαn αíkα....ídαn вα kαчí kα вαdα gurí dσmín вαnα ч'αr uwα kumα αвσkíчαr αíkí tα zσ dα wαní ѕαвσ mαí tαfє dα ѕαвσn ѕαlσ......_ _kαdα kují ínαtα zuвα ѕurutu gαmє dα в'αв'αtu вα kσwα nαkє nufí вα fαcє *AUNTY MAIMOUNATH O.G* dσmín kuwα вαnαmα tα dαwσ muku dα ѕαвσn nσvєl nαtα mαí cíkє dα dαrαѕí,ílímí,fαd'αkαrwα tαrє kumα dα k'αчαtαrwα ku nєmí nσvєl єntα mαí tαkєn *MEELAT TAMU*..._ _dαurє kα/kí nєmí nαkí α duníчαr ❄ domin kαdα α вαku lαвαrí........kαdαfα ku mαntα dα ѕunαn...._ *MEELAT TAMU.!* *MEELAT TAMU.!!* _ku nєmα ku ѕhα kαllσ tαrє dα kαrαtu,kαdα ku ѕαkє α вαku lαвαrííííí..._ *~__________________________~* _jínjínα tαrє dα gσdíчα gαrєkí mαruвucíчαr zαmαní *HALISSA ADAMOU* ч'αr mutαn nígєr mαвucíчαr *MARAYUMA Y'AY'A NE* kí jímα kíчí k'αrkσ tαwαn αllαh чα k'αrα míkí lαfíчα dα níѕαn kwαnα mαí αmfαní.. *SMASHER & HUBBEEY* nα gσdíчα dα kαrrαmαwαrkí gαrє ѕu.αllαh чα вαr zumuncí._ *~__________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ 5⃣3⃣ *K* asa controling temper ensa yayi wanda shi ne babban dalilin da yasa shi baro gurin ko tsayawa jin sauran d'aurin auren baiba ya baro gurin,bai zarce ko inaba sai gida wanda ikon Allah kad'ai ya kai shi,gidan a cike yake da jama'a amma sam BB bai iya gane abunda ke gaban sama bare kuma magana da ake masa da bai sanma suna yiba bare ya iya basu amsa. Bedroom ya shige nan ko ya shiga watsi da kayan jikinsa d'aya bayan d'aya har ya gama raba jikinsa da kayan ya rage daga shi sai singlet da wandon kayan kifewa yayi a k'asa take wasu hawaye masu matuk'ar k'una suka shiga tsere a saman fuskarsa,a wannan yanayin duk wanda yaganshi dole ne ya tausaya masa saboda ganin garjejen saurayi majiyin k'arfi yana kuka da hawaye dole abun ya baka mamaki game kuma da tsoro coz irin su ba komai ke sasu yin kukaba. Damuwa ta tarun masa gami da dana sani wacce bata da amfani,a dai-dai wannan lokacin da kowa ke cikin farin ciki da wannan ranar mai cike da tarihi,amma sam a gurin BB babu wannan labarin sai yanzun ya tabbata da ya tafka kuskure game kuma da asara wacce ba zai tab'a samun hanyan da zai gyaraba. Babu abunda yake banda wani irin haki mai ban tsoro idanunsa sun canja launi zuwa jaa mai duhu,kwanciya yayi nan k'asa dafe da k'irjinsa da yake jinsa kamar zai tarwatse saboda azabar ciwo da yake masa.... *GURIN 'DAURIN AURE.* Bayan fitowar su KHALEEL lokacin an gama d'aurin aure,Nanfa yayi ta dubawa bai ga BB a gurinba duk yadda yaso ya ganshi abun ya faskara,ko da ya tambaya wad'anda suka ga fitarsa sun sanar masa ya jima da fita,ko da yaji haka k'ok'arin kiransa yayita yi amma wayoyin sai ringing suke ank'i d'auka,duk k'ok'arin da yayita yi babu amsa,hak'ura yayi amma kuma hankalinsa baya tare da shi,kawai dai jama'an da suka kewaye shi ne yasa bai tafi nemansa ba dan yasan ba k'aramin abu ne yasa shi barin gurinba kuma har ya hana shi d'aukan kiransa. Haka suka wuce gurin reception daga nan,har akayi aka watse abokai da y'an uwa sunata musu Allah ya bada zaman lafiya,ana gamawa ko bai zarce ko inaba sai gidansu BB,direct d'akinsa ya nufa dan yasan can ne kad'ai zai sameshi. Abunda ya gani ya matuk'ar bashi mamaki game da tsoro wanda baiyi tsammaniba,magana ya shiga yi masa a hankali BB dake kwance k'asa ya d'ago rinannun idanunsa ya kalleshi da sauri kuma ya maida kansa ya kwantar wanda gaba d'ayan veins na kan sun gamaa bayyana. "Hasbunallahu wa-ni'imal wakeel....! KHALEED lafiyar ka k'alau kuwa,me yasa kake son zama cikin damuwa? me yake damunka ne kam...?" Banza yayi masa saima kulle idanunsa da yayi dan bai shiryawa jin maganganun KHALEEL enba yanzun da yake cikin wannan halin Jiki a sanyaye KHALEEL ya nemi guri ya zauna,a zuciyarsa ya furta "Ya kamata na sanar masa yanzun ko kuwa....?" Da hanzari kuma cikin tausayi ya kalli BB yana fad'in "Tashi za muyi magana yanzun..." Banza ya sake masa,hannunsa dafe da kansa da yake barazanar tarwatsewa,hakan da yayi masa yasa shi sake kallonsa,duk k'ok'arinsa na ya kwantar masa da hankali yasa shi kuma magana dan ya kore masa damuwan hakan ya faskara dan Sam yak'i bashi had'in kai,wayansa ya shiga pressing cikin apps nasa ya binciko app na *MAHEER MU-AQQILIIY* sauka ne complete amma a app yake nan ya kunna tun daga fatiha suke sauraro tare a lokacin da kuma suke zaman kurame,yini guda sallah kad'ai ke tada su,itama nan suke yinta cikin d'aki babu mai fita,weeding pics da ake da amarya da ango saboda tarihi a wannan ranar kama sam amaryar KHALEEL bata sashi a idanuntaba,dan ko suna can zaman makoki shi da aminin nasa... B'angaren AMARYA KHUBRA ko tun bayan da aka dawo da labarin an d'aura aure ta dad'a lafkewa kan bed dan ko dama tuni take fama da matsanancin ciwon kai wanda ya saukar mata da zazzab'i mai zafin gaske. Da k'yar aka samu ta iya shiryawa shima sai da taimakon ZUHRA,tana kwance ZUHRA na gefenta labarin d'aurin aure ya riskesu,jikinta ko ya sake rikicewa,tana kwance cikin duvet amma kana hango yadda jikinta ke vibrating kamar wacce aka jonama shocking. Duk k'ok'arin da MAMA take akan samun su KHALEEL a waya hakan ya faskara kan dole ta kira line en ABBA,shi enma dai suna tare da mutane lokacin da take kira dalili kenan daya sa bata same shiba,k'arshe dai sai magani aka bata haka da k'yar da sid'in goshi zazzab'in ya sauka sai ciwon kan da yak'i tafiya coz dama haka ciwon kai yake mata baya saurin tafiya idan ta fara. Shirin dinner ake sai daifa har lokacin babu ANGWAYE bare kuma AMARE duk iya kaiwa ruwan da za ayi anyi akan shirya KHUBRA amma sam ta kafe akan ba inda zata,k'awayensu ASHNA da ZUHRA da su suka zama k'awayensu duka a gurin,haka suka shirya suka d'auki hanyan tafiya dinner,ZUHRA aka bari gida dan ta kafa ta tsare akan babu inda itama zata idan babu KHUBRA a wajen,har aka dawo daga dinner suna d'aki ZUHRA na kula da ita,yini guda babu wani abu da taci duk k'ok'arin da MAMA tayi akan taci wani abu amma ta gagara yin hakan kan dole suka kyaleta kowa ya sa mata ido sai sannu da take karb'a daga bakin mutane da dama.Wajen 9pm aka fara dawowa daga gurin dinner dan d'aukan amare a lokacin ne kuma MAMA ta sake shigowa gefen da su KHUBRA suke,a kan idanunta ta shirya duk jikinta a sake kamar wacce bata da laka har ta kammala,kayansu tunda aka fara biki iri d'aya da ASHNA. Kusa da ASHNA aka zaunar da ita nan nefa ta d'ago idanunta da suke masu kama da an tsoma a man gyad'a tabi mutanen da kallo,KAKA ne zaune saman sofa sai sauran BAFFANINSU da kuma ABBA'NTA da ABBA'N BB,sai sauran y'an uwanta ZUHRA,FATAHIYYA,duk taurin kai da nunk'ufurci irin na BB da yake wannan kiran na manya ne sai daya halarta,cikin wani shigan daban sai k'amshi yake bazawa kamar sabon ango,fuska a d'aure kamar wani BOSS yake zaune gurin,ganinsa a gurin ya tabbatarmin yanzun kam da sauk'i jikin nasa sai dai har lokacin ba wani sosaiba sauk'in saboda yadda yake tafiya a hankali kuma cikin dauriya yake saboda bai son a gane halin da yake ciki. Bayan dogon lokaci da KAKA ya d'auka yana musu nasiha mai ratsa jiki,sannan sauran iyaye suka d'ora nasu,bayan nan kuma KAKA yasa akayi addu'a wanda ya dad'a sanyaya musu jiki daga bisani kuma akayi musu fatan zaman lafiya sannan aka fita dasu kowacce sai kuka take,a haka aka dangana da kowacce d'akinta. Amare sai muce Allah ya bada zaman lafiya... BB ne ya mik'e zai fito daga parlor'n KAKA ya dakatar da shi ta hanyar fad'in "To MALAM sauran kai ko naji ance ko budurwa baka da,ko dai a k'auye zan bada kai sadaka ne...?" Murmushin k'arfin hali yayi ba tare da yayi magana ba har KAKA ya gama jansa da tsokana wanda k'arshe shima ya biye masa,daga bisani kuma KAKA yayi masa nasiha sosai,shi dai sai mamaki yake ko mene dalilin wannan nasihar ta KAKA oho,haka har ya samu KAKA ya sallameshi,yana fitowa ko KHALEEL na kiranshi babu yadda zaiyi kan dole ya d'auka saboda yanzun ba kamar da safe ba jikin da sauk'i kuma tunanin da yayi ne akan rashin dacewar abunda yakewa KHALEEL en ya rinjaye shi,dalilin kenan daya yanke shawaran sakin jikinsa d'aukan wayan yayi,KHALEEL ne ya fara magana cikin sanyin murya "MAN! kana ina ne yanzun...?" Shiru yayi na d'an lokaci kafin ya iya yin gyaran muya sannan a tak'aice ya furta "Gida......" "Ok Zaka iya rakani ko kuwa....?" Jim ya sake yi kamar kuma bai gane mai KHALEEL en yake nufiba ya furta "Ina kenan..?" Cike da zolaya ko KHALEEL ya ce "Sai da kai zanyi..." "Uhmmm! kaima kasan na wuce haka ai" "Banda kuri dai.." "Haba wane irin kuri kuma kaima kasan gaskiya ai" Sai da KHALEEL yayi dariya sannan ya furta "Kawai dai ka shirya yanzun zan zo zaka raka ni wani waje ne mu dawo..." "Haba MAN ina zamu kuma a wannan lokacin kai da kake da amarya bai kamata ka barta taita jiranka ba kaga dare na dad'a yi,ka bari zuwa wani lokacin ka je koma ina zaka.." "To wai kam ina ruwan ka da maganar amarya ko kuwa shi kenan babu wani uzuri da zai taso min yanzun nayi kafin na wuce gidana...?" Banza BB yayi masa cikin sanyin murya kuma kamar wanda bai son magana yace "Za kayi ka bari d'an air kawai..." Sarai KHALEEL ya jishi kawai dai baison BB en yace ya fasa rakashin ne yasa yace "Naji...ni dai gani nan a hanya zan zo na d'aukeka.." Yana gama fad'an abunda zai fad'a ya datse kiran ba tare da yaji amsan da BB zai bashiba,cikin k'ank'anin lokaci kuma ya k'arawa motan wuta zuwa gidan su BB en. A harabar gidan ya tadda shi tun da suka gama waya ya kasa barin gurin har lokacin kuma yana jin chest ensa ba daidaiba duk da dai ya bawa kansa hak'uri amma kam yana jin zuciyarsa na k'aik'ayi kawai dai k'arfin hali yake. Yana daidaita parking BB na isowa kusa da shi cikin shiga kamar ta d'azun yanzunma haka suke har mamaki BB yayi daya ga KHALEEL sanye da irin kayansa wanda suka kasance kyauta daga gurin ABBA'NSA,bai tambaye shiba ya b'oye mamakinsa ta hanyar d'auke kansa daga kan KHALEEL en ya shiga motan suka bar gurin. Tafiyan babu wani nisa daga gidan su zuwa inda suka je en,a bakin wani gida KHALEEL ya tsaya sannan yayi horn,bud'e masa k'ofar get man en yayi nan ya danna hancin motan ciki,farfajiyan babu laifi akwai girma dan ko yanayin gurin zai tabbatar da hakan duba da yadda motoci da dama suke a parke a gurin,fita sukayi tare da kama hanyan shiga gidan KHALEEL na kan gaba sai BB dake bayansa,shi dai binsa kawai yake ba tare da yayi masa tambayan komai game da inda suka zo enba,har suka k'araso kusa da inda taron abokan nasu suke a cikin parlor. A nan ne kuma mamakin BB ya kasa b'oyuwa duba da yadda suka tarar da wasu daga cikin abokansu ke zaune,mamakin dake kan fuskarsa ya kautar sannan suka gaisa nan ko suketa masa tsiyan basu ganshi gurin reception ba da sauri KHALEEL yace "Ammm! da yake ai kunsan k'anwarsa ce amarya to kuma bata ji dad'i ba shiyasa ya tafi ya wakilce ni a gurin..." "Eyyahhh! gaskiya ne aiko yayi maka babbar karafa.." Daga haka suka yi musu fatan alkahiri sannan suka yi sallama da su ba tare da sun jira ganin amarya ba suka kama hanyan maida jama'ah zuwa gida. Parlor'n ya rage daga KHALEEL sai BB suna zaune can BB ya kalleshi "Ko mene ne ma'anar yin hakan da kayi...? A nawa tunanin ba sai kamin haka zan san kana son na rako kaba,idan ka sanarmin gidanka zan rakoka zan gagara yi maka hakan ne...?" Banza shima KHALEEL en ya masa saima dad'a nutsewa da yayi cikin cousion yana turo hulansa saman giransa,wayansa a hannu yana danne-danne,zaman kurame suka ci gaba da yi inda yake ankara da BB daya gama cika kamar zai fashe saboda haushin banzan daya masa bai bashi amsaba. Jin gidan yayi shiru yasa KHALEEL ya mik'e tare da gyara zaman cap nasa yana fad'in "Muje ko naji alamun babu mutane a gidan..." K'wafa yayi sannan ya mik'e yabi bayansa,ta nan cikin parlor'n suka bi wani k'ofan daban,sai gasu a wani k'ayataccen parlor'n fiye da wanda suka baro,a nan BB ya nemi guri ya zauna KHALEEL ya juyo cikin d'an alamu na kamar yayi mantuwa ya kalli BB "Sorry MAN d'an jirani nan nayi mantuwafa.." Kallonsa yayi sannan yaja wani uban tsaki,KHALEEL dai bai jira jin me zai fad'a ba ya fice da sauri. BB na zaune yaji alamun tashin mota a fili ya furta "Lallaima GUY ennan koi d'an rainin hankali..." Kiran KHALEEL en ya soma yana zaune har lokacin a gurin,shi kuma KHALEEL yana ganin kiran BB yayi murmushi game da k'in d'aukan kiran coz time en ya isa bakin get ko fita baiyi daga gidanba,sai da ya tabbatar da ya fice sannan ya tsaya gefen hanya ya fiddo wayansa,dai² lokacin kiran BB ya sake shigowa da sauri ya d'auka ko kafin yayi magana BB ya rigashi "Wane irin iskanci ne wannan zaka ajiye ni ka fice...Ko kuma ka maidani mai tsaron gidanka ne...?" Dariya sosai KHALEEL yayi iya son ransa har saida BB yaji haushinsa "Idan ka gama gasamin maganar to ka shiga ciki matarka na jiranka..." Yana fad'in haka ya datse kiran,cikin rashin fahimta BB yake son tambayansa,anya kuwa yaji dai² ko kuwa dai kunnensa ne yake yaudararsa,kafin yayi magana yaji an katse wayan,k'ok'arin sake kira yayi amma KHALEEL yak'i d'auka har ya gaji da kira dan kansa ya bari.. Ganin bai sake kiraba KHALEEL en ya tafa masa text kamar haka... _Am sorry friend naso yi maka bayani tuni sai dai kak'i amincewa muyi maganar shi yasa ni kuma na yanke shawaran yi maka haka,tabbas nasan a yanzun kana cikin shock da maganar da na maka,sai daifa tabbas abunda na fad'a babu k'arya ko zolaya a ciki,dama kai na rako ba wai ni ka rakoba,ina maka fatan alkhairi kai da amaryarka *KHADIJATUL-KHUBRA*.Na barka lafiya aci amarci lafiya._ *UR'S KHALEEL.* Dai² lokacin daya samu sak'on bayan ya gama karantawa mik'ewa yayi tsaye kamar wanda aka tsikara yana nanata sunan *KHUBRA* da ya gani rubuce............... *COMMENT FOR MORE PAGE'S......* 💃💃💃 *~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~* *_®єαl $mαѕhєr._* 😉 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/ *©®2018* *26/ʝųlყ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~__________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ 5⃣4⃣ *S* till yayi a inda yake har lokaci he ain't believe abunda yaji kuma ya gani gaske ne,cap nasa yayi removing ya cilla saman cuition shi kad'ai sai kaiwa da kawowa yake cikin parlor,zuciyarsa tak'i samun nutsuwa da abunda KHALEEL en ya sanar masa,nan ko ya shiga magana a fili "How za ace haka ya faru bayan akan kunnena naji d'aurin auren wannan kawai shirme ne na sani irin na KHALEEL babu yadda za ayi haka ya faru,am not believing any more...." Waya ya sake dannama KHALEEL,ganin kiran BB yasan da akwai damuwa kan dole ko ya tsaya gefe still yayi yana sauraron maganganun BB da yake yinsu cikin fad'-fad'a "Heyy! MR MAN u have to came and take me up here right now..... Banda shirme irin naka taya za a d'aura maka aure da yarinya naji kuma akan kunnena ka maida ni wani sauna....Idan ma baza ka dawoba to zan bar maka matarka cikin gida,and ni kuma na san inda dare yamin..." "Ka gama fad'an....?" KHALEEL ya tambaya cikin coolness tone "Ohhh! abunda za kacema kenan...wato ka mai dani wani tamkar ban san abunda nakeba shi ne harda cemin na gama fad'an....? To ban gamaba kuma Allah ka ji na rantse babu abunda zai hanani tafiya,idan ka gama ka dawo ka tarar da babu kowa...." Yana kaiwa nan ya datse wayan ko sauraron me KHALEEL en zai fad'a baiba kuma har lokacin yana tsaye sai huci yake. KHALEEL jin da yayi BB ya kashe wayan yasa shi saurin yin tunanin ya kamata ya tura masa wani evidence da zai zauna cikin gidan kada ya bar yarinyar mutane ita d'aya a gidan,da saurinsa ko ya tura masa sak'o ta email,sannan ya jaa motansa ya k'ara gaba. Dai² lokacin da yake sintiri tsakiyan parlor hannunsa d'aya a dunk'ule yana naushin iska sak'on ya shigo,da sauri ya isa kusa da phone en yana dubawa,email nasa ya shiga cikin sauri saboda ganin sak'on ta email yake,nan ko ya tarar da sak'on audio da kuma na video's wanda da gani babu tambaya kasan a gurin d'aurin aure ne. Cikin hanzari ya shiga playing nasu d'aya bayan d'aya yana kuma sauraro har dai² lokacin da aka soma sanar da d'aurin auren kamar haka _An d'aura auren *IBRAHIM KHALEEL* da amaryarsa *KHADIJATUL-KHUBRA* akan sadaki naira na gugan naira har naira dubu d'ari biyar..._ Wani uban tsaki BB yayi a dai² nan yana fad'in "Banda d'an iska ni zai rainawa hankali kamar ba a gabana aka fad'i hakaba...." Kafin ya sake magana yaji mai sanarwar yana fad'in _"Afwan..! Afwan..!! Afwan..!!!_ _Y'an uwa a gafarceni nayi makuwa gurin sanar da wannan d'aurin auren,ina fatan kuma za amin afuwa dan kuwa ba *KHALEEL* zan ambataba gurin fad'amin ne aka samu sab'ani sai yanzun aka sanar dani gyaran dake cikin wannan maganar tawa,a maimakon KHALEEL dana ambata *KHALEED* ne angon,wannan auren na *KHALEED* ne da amaryarsa *KHADIJATUL-KHUBRA*_ _Sai kuma auren *IBRAHIM-KHALEEL* da amaryarsa *FATIMA-ZUHRA* akan sadaki dai-dai dana y'ar uwarta,aure na uku kuma shi ne na *ABUBAKAR-SADEEQ* da amaryarsa *ASHNA* sadakinta kwatankwacin na y'an uwanta lakadan ba ajalanba...._ Dafe baki BB yayi yana fad'in "Ta yaya akayi haka ya faru? kenan bayan na bar gurin akayi haka ko kuwa yaushe ne hakan ya faru...?" 'Daya bayan d'aya ya dinga binsu yana playing har yazo na k'arshe,again bai hak'ura ba ya sake kiran KHALEEL,shima cikin isa ya d'auka yana fad'in "MAN! lafiya kake kirana kuma dai² lokacin da zan shiga gidana? ko kuma har yanzun shaidan basu gama gamsar da kai bane...?" Murmushi kawai yayi yana fad'in "Noo! kawai dai na kasa yarda ne...!" "To tunda baka yarda ba ai shi kenan ka jira gobe sai su ABBA su maka bayanin yadda akayi haka,ni nayi iya nawa sauran nasu..." Yana kaiwa nan ko ya kashe wayan gaba d'aya dan yasan idan ya barta haka BB zaita damunsa da kira,dai² ya shigo parlor aiko ya juya ya kulle k'ofofi tare da addu'an neman kariya daga mahalicci... ********** B'angaren amarya KHUBRA kuwa tun bayan da suka futo daga parlor lokacin za a sasu mota ta rik'o ZUHRA akan itafa lallai sai dai k'afarta k'afar ZUHRA zasu tafi,ganin zata jik'a musu aiki da dabara aka sata cikin mota sannan aka ce to ta matsa ZUHRA ta shigo,da yake babu wayo nan ko ta matsa aiko tana yin haka aka rufe k'ofan sannan driver'n yaja yayi gaba. Kuka babu irin wanda bata yiba dan an taho da ita babu ZUHRA dama kuma ba wani cikakkiyar lafiya gareta ba,haka ko bayan da aka kawota da d'aya da d'aya duka suka zare jikinsu suka gudu,aka barta daga ita sai halinta,kukanta ta shak'a bayan taji gidan shiru a nan inda ta gama kukan take kwance jikinta duk ya dad'a yin zafi tana saman bed jikin ta ya ko dad'a rikicewa .... Nan parlor yaci gaba da zama ya kasa yanke shawaran abunda ya kamata yayi,har 12am yana nan shi bai bar gurinba kuma bai daina kiran number KHALEEL ba duk kuwa da yadda wayan ke sanar masa a rufe take,wani zuciyan ne ya bashi shawaran kiran UMMI baiyi tunanin komaiba ko yaddana mata kira ba tare da yayi tunanin dare yayi ko akasin hakaba... Cikin magana irinta mai bacci UMMI ta d'auka tana fad'in "KHALEED SON lafiya kuwa ka kirani cikin wannan lokacin.....ina ita KHUBRA'N ko kuwa jikin nata ne ya sake rikicewa...?" Murmushi yayi mai k'ayatarwa ko tantama babu yanzun kam ya soma gasgata maganar KHALEEL,sai dai tambayan da yake ta damun kansa shi ne *TA YAYA HAKA YA FARU?*. Murmushi yayi ta saki abunsa kamar ba wanda yake jinya ba d'azun,kan cuition ya kwanta had'eda kashe wayan ba tare da yayi magana ba,yana juya lamarin a ransa,lallai a yanzun kam ya tabbatar da komai hukuncin rabbi ne ba tare da dabara ko k'arfinsa ba ya bashi abunda ya jima a ransa a kuma lokacin da babu zato bare tsammani, ai kam ya tabbatar a yanzun yafi kowane d'a namiji sa'a,a duniyarsa gani yake babu wanda zaiyi dace kamar nasa. Tunawa yayi da maganar KHALEEL ta d'azu da abokansu suke tambayan basu ganshi gurin d'aurin aureba,sannan kuma maganar UMMI ta sake fad'o masa inda take cewa _"KHALEED SON lafiya kuwa ka kirani cikin wannan lokacin.....ina ita KHUBRA'N ko kuwa jikin nata ne ya sake rikicewa...?"_ Cikin hanzari ko ya mik'e yana bin hanyan da zai sadashi da d'akunan baccinsu cikin damuwa coz bai san halin da take cikiba a fili ya furta "Is she ill...? Amma tun yaushe ne hakan ya faru...?" Dai² lokacin ya iso kallon gefe da gefensa yayi coz bai san a wane room take ba,kallon doors yayi ya d'an tsaya tunani can kuma sai ya kalli wanda yake bud'e a hankali ya d'aga k'afafunsa ya nufeshi... *GIDAN KHALEEL...* Bayan ya gama tura masa abunda zai tura daya kashe phone ensa ya kulle k'ofifi,hanyan bedrooms en ya nufa yana fad'in "HABIIBTIIY!!!.....Ina kika shige ne..?" Shiru yaji babu amsa nanko ya nufi cikin bedroom enta,zaune saman bed ya hangota sai dad'a jan vail enta take tana dad'a rufe jikinta,da alama da ba gurin take zauneba,dariya yayi yana fad'in "Ohh! kunyana kuma ake ji yau..? i think yau kam babu wannan a tsakaninmu tunda burin da muka jima da shi yanzun Allah ya nuna mana ranar da muketa jira...So ina ganin kamata yayi ace munyi godiya ga Allah daya nuna mana hakan cikin rai da lafiya gami kuma da kwanciyar hankali..." A hankali ta d'an motsa kamar zata janye vail en sai kuma yaga sab'anin haka "Ohhh! wato sai kin bani wahala dai kenan ko..?" Har lokacin ZUHRA ta kasa masa magana,ta kuma k'i d'agowa ta kalleshi,saman bed en ya isa yana ajiye ledan dake hannunsa,a kusa da ita yayima kansa masauki,fuskanta ya shiga lek'awa yana fad'in "Haba mana duk kalaman da nake GAM DA KATAR (ZEEY BUGAJE) dasu a kullum kuma yauda nake tsammanin ganinsu a zahiri bayan tsawon lokacin da muka d'auka bama tare,sai naga sab'anin haka,shi kenan tunda baki son ganina bari na koma inda na fito...Dama na had'u da wata d'azun so kinga saina tafi zance gurinta ko?" Yana gama fad'in haka ko ya shiga k'ok'arin mik'ewa da niyyan zai fice,a zahiri kuma yana kallonta yaga wane reactions zata bayar da jin maganar tasa,alama yayi kamar zai fice,aiko nan ZUHRA ta dire k'afafu tana bugasu k'asa cikin tab'ara tana fad'in "Ni wallahi a'a,kuma idan ka fita nima saina bika duk inda zaka..." Dariya ya kwashe mata da,sai da yayi son ransa,ita kuma ganin yana mata dariya gashi dama tunda ta mik'e tayi cilli da mayafin,tsayawa tayi kallonsa yadda yake dariya take kallo sai taga ya k'ara mata kyau fiye da yadda ta sanshi.Tsayawa tayi tana kallonsa bata k'i su dawwama a hakaba. Ankara yayi da irin kallon da take masa,nan ya matsa kusa da ita,waist enta ya rik'o yana matso da ita jikinsa,da sauri ta kalleshi coz batama san ya akayi yazo kusa da itaba,jinta da tayi a jikinsa shiya farkar da ita,duk'owa yayi dai² kunnenta yake fad'in "MADAM wannan kallonfa haka,bayan gani kusa da ke,ko mafarki kike yine wata ta k'wace miki ni...?" Kai ta sake d'agawa ta kalleshi jin abunda ya fad'a,a hankali ta tab'e d'an bakinta ta sake kauda kanta,mutsu-mutsu ta shiga yi saboda tana son ya saketa,shi kuma hakan da tayi yasa shi dad'a rik'eta sosai "Please YAH ka sakeni..." Maganar yayi escaping daga bakinta ba tare da ta shiryama hakan ba. "Nak'i...Ina son jina jikinki ne yasa..it's been long da nake son mu kasance tare sai dai aikin UMMI ya hana mu kasancewa kusa da juna....Buh Al-hamdulillah alaa kulli haliin...Yau kam komai ya zama tarihi,tunda gamu yanzun a matsayin abu guda.." 'Dan murmushi ta sake yi tana sauke kanta k'asa dan ita kam yanzun tunda ya fara mata wannan maganar take jin kunyarsa... 《《》》 Shigansa d'akin ya hangota can saman bed ta duk'ule guri guda,jikinta sai karkarwa yake da alama dai kam tana cikin mawuyacin hali,da d'an hanzari ya isa kusa da ita nan ya birkitota ta juyo suna fuskantar juna sai dai nata idanun a kulle suke,jikinta sosai yayi zafi fiye da tunanin mai tunani saboda hatta da kayan dake sanye jikinta hucin jikinta ana jinsa jikin kayantan. Tsayawa yayi dafe da hab'ansa yana tunanin me ya kamata yayi mata wanda zai sauke mata zazzab'in,a hankali ya kad'a hannu sannan ya nufi toilet,bowl ya d'auko a toilet ya d'ebo ruwa,dawowa yayi ya d'ora shi saman side drower sannan ya nufi wall-drop,k'aramin towel ya d'auko ya dawo kusa da inda dake,nan ko ya soma tunanin me zaiyi kuma..?,Ganin yana b'ata lokaci kuma gashi har lokacin jikinta na a yana yin daya taddata yasa a hankali ya haura saman bed en har lokacin ya kasa believing da abunda yake shirin aikatawa,hannunsa sai rawa yake kome ya tuna kuma yayi saurin janyota had'e da soma rabata da kanyan jikinta daga ita sai pant da bra ya barta,bowl en ya janyo nan ya sa towel en cikin ruwan ya matse,goge mata jiki ya shiga yi sai rolling eyes nasa yake a kanta,ganin batama san me yake yiba,har yayi ya gama bata san halin da take ciki bama bare tasan waye a kanta yasa ya kauda tunanin dake ransa . Kwantar da ita yayi yaja duvet ya rufeta da shi,sannan ya tafi maida kayan da yayi amfani dasu,ruwan ya zubar ya wanke bowl en sannan ya maida shi muhallinsa,fita yayi a d'akin ya nufi d'ayan bedroom en,sai da ya gama shirin kwanciya ya tuna da halin daya barta,da sauri ya diro daga saman bed en dan a time en har yayi addu'ah ya fito ya nufi d'akin nata dan ya duba halin da take yanzun kafin ya kwanta. Zafin jikin kam alhamdulillah da sauk'i sai dai har yanzun tana nan a dunk'ule kamar d'azun da alama kuma sanyi take ji,tsayawa yayi ya rasa me zai yi kuma,d'an gajeran tunani yayi tunawa da wani india'n film,d'an murmushi yayi daya kalleta had'e da shafa kansa ya haura saman bed en,sai daya tabbatar da ya dai-daita zamansa saman bed en sannan a hankali ya zuge zip na pyjames ensa a hankali yasa soft hands ensa ya janyota,cikin jikinsa ya sata sannan ya maida hannayensa ya zagayeta da dasu,a hankali ta sauke wani wahalallen ajiyan zuciya,shi kansa BB jinta kwance cikin jikinsa sai da yaji bak'on al'amari a tare da shi.Ranan kam da kyar ya iya bacci saboda ya tsinci kansa cikin yanayin da ya kasa tantance na mene ne,farin ciki ko kuwa akasin haka.... 《《》》 *GIDAN SADEEQ BIGGY.* Aifa a wannan dare bayan watsewar y'an kai amarya ango ya shigo shi d'aya ba tare da ya yarda kowa ya rako shiba,haka ya tadda sahibar tasa ta hakimce da alama kuma zuwansa kad'ai take jira.. Bayan sun gabatar da komai cikin ilimi,wanda ita kanta ASHNA sai da angon nata ya bata mamaki jin yadda yake rero k'ira'a,after kuma yaita zuba addu'a ita dai a zuciyarta take fad'in "Allah na gode maka daka sa mijina yake da ilimin addini,amma abun mamaki dama haka yake da ilimi...? A da kam nayi tsammanin bashi da komai,ina masa kallon irin mutanen da suke fama da k'ungurmin duhun jahilci.." Kallonsa ta sake yi a karo na biyu ganin sun had'a ido yasata saurin sunkuyar da kanta,a haka suka gama duk abunda za suyi a wannan dare sannan suka kwanta,kwanciyarsu babu jimawa ta tsinkayo hannun BIGGY a jikinta yana murzarta,nan ko jikinta ya hau rawa dama kam tasan da kamar wuya ya d'aga mata k'afa a yau,tana tunani shi kuma yana ci gaba da aikin da yake gabansa,a haka har ya samu daman da yake buk'ata bai tsaya b'atawa kansa lokaci ba ko ya amsheta da hannu biyu-biyu..... Ko a gidan KHALEEL ma hakan ce ta faru tsakaninsu,wanda a wannan dare ZUHRA kam tayi kuka iya yinta,KHALEEL duk ya wani dad'a rikice mata a haka har ya samu abunda yake nema a tare da ita,sai bayan da ya samu nutsuwa tukun ya koma lallab'ata kamar kwai yana kuma sa mata albarka sai sumbatu yake zuba mata,bayan komai ya lafa kuma ta koma tausayawa KHUBRA a ranta take fad'in "Allah sarki CWEETY yanzun kam nasan babu lallai BB ya mata komai saboda nasan idan har yaganta a yanayin da muka rabu tabbas zai tausaya mata bazai mata komai..Allah ya baki SISTER'NA" A haka suma bayan ya tsaftacesu suka kwanta cike sa so da k'aunar juna yana rad'a mata maganganu masu dad'i da kwantarwa da mutum hankali...... 《《》》 Sai da gari yayi haske sannan KHUBRA ta farka,jinta jikin mutum ta shiga k'ok'arin zare jikinta saboda haske da take gani cikin d'akin ya tabbatar mata da an jima da yin salla'n asubah.. Motsinta ne ya farkar da shi,a hankali ya bud'e idanunsa ya saukesu a kanta,d'an murmushi yayi ganin idanunta a kulle kuma sai k'ok'ari take ta tashi,fuskarsa ya gintse sannan ya saketa,da sauri ta mik'e ta fito a cikin duvet en,k'afafunta ta zuro k'asa tare da bud'e idanunta,kallon jikinta tayi ganinta daga ita sai pant da bra yasa ta k'walla k'ara had'e da saurin yayibo bargon ta b'oye ciki. Murmushi yayi ta zubawa,yana kallon yadda ta shige tak'i fitowa,mik'ewa yayj ya fice a d'akin jin an rufe k'ofa tayi saurin lek'owa tana duba d'akin ganin babu kowa tayi wurgi da bargon,a guje ta shek'a had'e da rufe k'ofa harda murza key,sannan ta dawo a bakin bed ta zauna tana maida numfashi,hakan da tayi niko nace _"Ehh! lallaifa KHUBRA kin samu sauk'i...tunda gashi harda su gudu bayan ihu.._ Tunawa da bata yi sallah ba yasa tayi saurin tashi tayi hanyan toilet,wanka ta fara yi sannan ta d'auro alwala ta fito,doguwar riga ta zura ajikinta tayi sallah,bayan ta idar ta jima tana addu'o'i. Knocking k'ofan da akayi yasa ta dafe chest enta tana jan numfashi da sauri kamar wacce taga abun tsoro.. Muryansa yasa ta dad'a fiddo ido waje ko a mafarki kam taji shi zata gane waye bare kuma ido biyu,dafe bakinta tayi idanunta sun dad'a bayyana tace "BB kuma....? me ya kawo shi da wannan safiyan kuma...? Ina YAH KHALEEL en ya shiga bayan fitansa daga nan...?" Ita kad'ai ta rasa mai bata amsa,kuma har lokacin batayi yunk'urin yin maganaba,sai data tabbatar da ya bar gurin sannan ta matso jikin k'ofan,a hankali ta bud'e tana lek'awa. "Yeehhhh! AUNTY AMARYA..." FATAHIYYA dake tsaye ta fad'a,a d'an tsorace KHUBRA ta kalleta "Wallahi har kin bani tsoro..." Dariya tayi mata sannan ta bud'e k'ofan tana juyawa ciki bayanta ta biyo dai² lokacin suka gaisa a hankali tace "Ina ZUHRA'N kuma naganki ke d'aya.....Ko kuma dama keda BB kuka zo....?" Kallon rashin fahimta tayi mata bakinta bud'e take fad'in "AUNTY kika ce mene...?" "Ohh! da baki ji me nace bane kam?" "A'a naji mana kawai dai tambayoyin naki ne suka sani mamaki.." Kallonta KHUBRA tayi tana fad'in "Mamakin me kuma kan wannan y'ar tambayan...?" "Amm! to ai AUNTY naji kina tambayana ne kamar baki san komaiba..." Idanta tayi blanking sannan tace "Kamar yayafa....?" "Ehhh! Naji kina tambayana YAYA ZUHRA.." "Ehh! laifi ne dan na tambayeta gani nai bata zoba kuma bayan ita yafi dacewa data zo en..." Dariya sosai FATAHIYYA tayi sannan ta kalleta tace "Hala kam AUNTY baki san tana gidanta ba itama ko...?" A tsorace KHUBRA ta kalleta "Gidanta fa kika ce..? Wane irin gida kuma kike nufi?" "Uhmmm! gida dai na aure kuma irin wannan da kike ciki..." Jikinta duk ya dad'a shiga shock da jin maganar FATAHIYYA amma sai ta daure tana fad'in "To amma waye angon kuma ya akayi ni ban san da haka ba..?" "YAH KHALEEL ne...." Ta bata amsa a tak'aice. Ai tuni ta dad'a fiddo idanunta waje tana kallonta,ckin tsoro murya na cracking ta furta "Ni kuma wa nake aure kenan....?" A dake ko FATAHIYYA ta furta "BB mana...!" Ai jin haka take yasa KHUBRA tayi freezing a gurin hannunta a saman chest baki kuma bud'e.............. *COMMENT FOR MORE PAGE'S........* 💃💃💃💃💃💃 *~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~* *_®єαl $mαѕhєr._* 😉 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/ *©®2018* *30/ʝųlყ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~___________________________~* 🎂🎂🎂 _All I got you for your birthday was this post. Hope you enjoy it! Try not to read it all at once._ _May God shower his choicest blessings on you. wishing you happiness, good health and a great year ahead._ _Once more Happy birthday wish you fruitful years *HAFSAT M.U.(REAL HEARFSEY)*._ *Happy Birthday sweet sis.* 🎂🎂🎂 🎁🎁🎁 _Here is my gift for u..._ 😉 *~___________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ 5⃣5⃣ *I* danunta sun dad'a bayyana a fili saboda tsantsar tsoro da fargaba da suka taru suka mata yawa,a bakin bed en tayi ragwaf hannayenta tallafe da kumatunta,nan ta tafi duniyar tunani,d'an tak'aitaccen tunani tayi a hankali kuma ta kalli FATAHIYYA tana fad'in "Wato shi yasa tunda aka fara hidiman biki komai namu ya zama iri d'aya,ashe da walakin aka ce 'goro a cikin miya'....To amma me yasa za ayimin haka bayan ga wanda ke sona kuma a auramin wani daban...?" Kafin ta bata amsa BB ya shigo cikin bedroom en,fuskar nan a gintse kamar ba shiba,ya kallesu dukα tunanin KHUBRA a LOKACIN yaji abun da ta fad'a shi yasa tsilli² jin baiyi maganaba yasa ta saki ranta amma zuciyan tafa a lokacin banda skipping babu abunda take yi,sai k'amshi yake zubawa da ka ganshi zaka tabbatar da lafiya ta samu,a hankali ya juya yana daidaita zaman hulan a kansa ya furta "Idan kun gama ku sameni parlor.." Daga haka bai k'ara koda wasalin 'a' ba ya fice,a hankali KHUBRA ta tab'e baki kanta na k'asa tun shigowarsa SAI ajiyan zuciya da take,FATAHIYYA ce ta kalleta taga yanda take kamar a takure cikin salon tsokana tace "AUNTY kijefa kuyi break ni kam sai dana gama nawa sannan na fito,so ni kam a k'oshe nake...." Hararanta KHUBRA tayi kafin ta mik'e zata fita,da sauri ko ta rik'o hannunta tana fad'in "AUNTY ince dai ba a haka zaki fita gurin YAYA'N ba ko...?" "Mene to dan naje a haka..?" "Haba dai kingafa face naki ko lip stick babu bare kuma powder,ke kam dai ai kya gyara face naki kafin ki fita,amarya ai da kwaliyya aka santa..." "Ke ni da Allah kyaleni wane kwaliyyan zanyi kuma,ko dan ba auren so.....!" Kafin ta k'arasa FATAHIYYA ta katseta tana fad'in "Tabbbb! lallai AUNTY za kiyi wasa da damanki,ko kinsan da yawa y'an mata damar da suke nema kenan ko da basu son namiji zasu zauna da shi musamman ace yana da y'ay'an banki,bare kuma ace mijin yana da kyau....Kamar dai naki mijin...To wallahi AUNTY kiyi a hankali da mijinki dan idan y'an mata suka d'ora idonsu akansa sai dai kiji labarin ya canja salo,garama ki kamashi da hannu biyu-biyu ko da kuwa baki sonsa a hankali zaki fara sonsa..." Tunani ta d'anyi cikin y'an dak'ik'u,tabbas tasan duk abunda FATAHIYYA ta fad'a mata gaskiya ne,ko ba komai kuma d'an uwanta ne na jini,ko da ace babu soyayya to tabbas akwai y'an uwantaka,kenan ya zama dolenta ta kula da shi kamar yadda zata kula da kanta ko fiyema da haka.. A fili kuwa sai tayi murmushi ta kuma godewa Allah daya sa Y'ar uwarta ta bata wannan shawaran,a ranta ta k'udiri niyyan ko da bai sonta to lallai ita kuwa zata koya masa yadda zai so ta,a hankali cikin sanyin jiki ta mik'e ta nufi gaban mirror kallon kanta tayi ta ciki tabbas ita da kanta ta san mai kyau ce,amma ai ana cewa idan kana da kyau to ka k'ara da wanka,cikin y'an mintuna ta fente fuskarta cikin simple make-up,har ta tashi zata fita again FATAHIYYA ta sake dakatar da ita,closet ta bud'e nan ta ciro mata riga da sket na wani holland mai kalar ja da adon kore,babu musu ta sauya kayan sannan ta feshe mata jiki da turaruka iri daban-daban ta kuma d'aura mata head tie en,das ya zauna kamar ashobe a kanta,duk wanda yaga wannan kwalliya ji zai inama ya saceta ya gudu saboda kyau da tayi,ita da kanta data kalli kanta a mirror sai da tayi murmushi saboda yanzun kam tasan tafi yin kyau sosai,musmman jan kala data sa daya had'u da farar fata,plat shoe ta zira sannan tayi hanyan parlor ta bar FATAHIYYA nan tana ta yaba kyau da tayi kafin ta fita ko sai da ta gama kyasa mata pictures sannan ta barta tana danna phone.. Kwance yake saman cuition da phone a hannunsa sai murmushi yake zubawa,da ganin alamu kasan yana cikin yanayin da yake jin dad'insa,tun kafin ta bayyana a gabansa k'amshinta ya iso,a hankali ya lumshe idanunsa yana shak'an sanyayyen k'amshin turarenta,idanunsa a haka har ta bayyana cikin parlor dai² zata wucesa ta kalleshi ta sake tab'e baki ai ko nan suka yi four eyes da shi,fuskarsa ya d'aure ganin abunda tayi,zata wuce ya dank'o hannunta had'e da fizgota,kansa ta fad'o take ta runtse eyes nata chest enta na harbawa da sauri-sauri,yanda tayi yasa shi kallonta sannan ya d'an saki fuska,dai-dai kunnenta ya kai bakinsa cikin wani irin salo ya furta "Kina jin tsoro a kamaki kinyi laifi,amma kuma kin iya yin laifin ko...? Nan gaba idan na sake kamaki kin min wannan abun zanyi maganinki..Kin jini ko..?" A hankali ta d'aga masa kai alamar ta ji,idanunta har lokacin a kulle,eyes nata yake so ta bud'e ta kalle shi amma abu ya gagara,baya ga maganar ta daya ke son saurare,a hankali zuciyarsa ta bashi shawaran sata magana,rasa me zaiyi mata yayi wanda zaisa tayi magana. A hankali ya kai bakinsa dai-dai kunnenta yana hura mata iska ciki,da sauri ko ta bud'e idanunta tana kallonsa,hakan da tayi yasa shi d'aga mata gira,da sauri ta girgiza masa kai alaman babu komai,ci gaba yayi da abunda yake,cikin voice nata mai nuni da wanda ke magana yana cikin wani hali ta furta "YAYA ka bari..." Kallonta yayi yana murmushin gefe "Ohhh! da kina da baki kika d'aga min kai kaman wata lizard,ko kina ciwon hak'ori ne...?" "Ni lafiyata k'alau..." Ta k'are tana murgud'a masa baki,bata k'are abunda take son fad'a ba,ta tsinci d'an mitsitsin bakintan na futsara a nasa,sai da ya tsotse lip bam nata data sa tas,dan kansa kuma ya sake mata baki,sai dai har lokacin tana rik'e a jikinsa ai ko ganin yak'i sakinta har lokacin ga kuma tarin kayan kunya daya barta da shi yasa ta b'oye face nata a jikinsa,tana maida numfashi da d'aya da d'aya. Tana kwance jikinsa shi ko babu abunda yake sai sakin smiling jinta a jikinsa yafi masa komai a duniya,bai k'i su dawwama a haka ba,da sauri kuma ya dakata da murmushin da yake saboda wani tunani da zuciyarsa ta bijiro masa da shi "Shin ma wai kai da kake wannan zumud'in ka tabbatar da yarinyar nan na sonka ne ko kuwa kai kad'ai kake kid'anka kake kuma rawar....Wannan rawar kan da kake idan kuma yarinyar ba wani sonka take bata,shi kenan ka yada girmanka?" 'Dan sassauta rik'on da yayi mata yayi,a zuciyarsa ya furta "Ya Allah ka taimaki bawanka a dai² lokacin da baiyi tsammani ba......Ya Allah ina rok'onka a karo na biyu kasa ba ni kad'ai ke fama da dakon soyayyanta ba..." Kallon mamaki KHUBRA ta bishi da shi tana fad'in "Ni ka sake ni na tashi,ka wani rik'e ni bayan kuma sai maganar kana son wata kake,to idan za kayi maganarka sai ka bari kayita kai kad'ai amma ka denamin ni dan ban son ji ni..." Ta k'arasa tana ture shi,kallonta yayi yanda tayi magana yasa shi sakin murmushi wato dai maganar da yayi a zuciyarsa a fili yayita kenan. Baya ga haka kuma mene ne dalilin daya sa ta fad'in haka,fuskarta kad'ai zaka kalla kasan ranta a b'ace yake,dan ya kauda zancen yasa ya saketa da sauri ko ta mik'e tana gyara riganta daya d'anyi squeezed ta gaba,cikin sauri ta bar gurin,shi dai kawai ya bita da kallon mamakin kalmominta. Har ta b'ace masa sannan ya sauke idanunsa yana murmushi lallai zai sha fama,dan kam ya tabbatar za tayi bak'in kishi da ganinta. Tunawa yayi da dalilin da yasa ta fito,gashi yanzun kuma ya koreta.Lallai ya zama dole ya kirata,sai yanzunma ya tuna da jiyafa ba wani lafiya gare taba a haka kuma suka kwana,amma yau ji yanda tayi masa kamar ba itaba,bedroom en nata ya nufa,nan ya hangota kwance ta juya baya,FATAHIYYA nata fama da waya a hannu,ganin shigowansa yasa ta tab'ota da sauri ta juyo tana kallonta,ganinsa cikin d'akin tayi saurin kauda kanta daga gurin "Kin taso kinyi break ko kuwa sai na maimaita miki warning da na miki..." Banza tayi da shi ita ko FATAHIYYA da sauri ta fice a d'akin,ganin tak'i kula shi yasa ya k'araso inda take cike da isa ya d'agota,sai da ya tsaidata a kan k'afafunta sannan ya furta "Oyaaah! muje muyi break sai na baki labarin abunda kike son sani..." "Na k'oshi ni..." "Da kika ci mene zaki fad'i haka...Maza wuce muje kafin na sab'a miki.." Bakinta ta kyab'e za tayi masa tab'ara,bai tsaya sauraronta ba ya kama hannunta suka fice.. Har suka kammala break fast bata sake kula shiba,shi ko duk spoon d'aya da zai kai bakinsa sai ya kalleta yayi murmushi,a haka har suka kammala,ita ta fara ture plate nata tana yamutsa face,yana kallonta bai ce komai ba har ya kammala,tattara kayan tayi sannan tayi kitchen shi kuma ya koma cikin parlor,da sauri FATAHIYYA ta tadda ita a kichen amsan kayan tayi taba fad'in "Haba AUNTYNAH ina nan kuma wane aiki za kiyi,kije ki huta bari na wanke kayan..." Murmushi kawai tayi tana mamakin halayen FATAHIYYA a yanzun kamar ba ita ce mai d'an banzan jin kannanba a da,da sauri kuma ta juya zuwa parlor. Tsaye ta same shi yana dad'a gyara cap nasa,tab'e baki ta sake yi da sauri kuma ta rufe bakin saboda tuna abunda yace d'azun tana kuma kallonsa,juyowa yayi yana kallonta dai² tana shirin zama cikin cuition. "Ammm! zan fita ga FATAHIYYA nan ku zauna tare zanje gida na dawo ba jimawa zanyi ba kinji...?" Kallonsa tayi tana mik'ewa tsaye "YAYA nima zani kaji....kaga jiya dama banga ZUHRA ba yanzun sai ka kaini gurinta..." Dariyar rainin wayo yayi kafin ya rik'o hannunta ya zaunar "Haba BABY waye ya fad'a miki amarya tana zuwa gida a irin wannan ranar..? kiyi zamanki nima ba dad'ewa zanyiba kinji...?" Baki ta kyab'e za tayi kuka,shi dariyama take bashi duk wani abu na yara ta iya "Noo! kada kiyi kuka kinji yanzun zan dawo,barima nayi sauri naje ina son mu had'u da KHALEEL ne kinji...?" Kai ta kad'a masa tana cuno baki,sakinta yayi da sauri kuma ya fice dan ya tabbatar idan ya biye mata to ko babu inda za shi,yana fita harabar gidan ya daidaita tafiyansa daga saurin da yake yi,KHALEEL ya kira yana fad'in "MALAM ai sai kazo ka d'auke ni ko,tunda kunmin auren dole kuma name ne na wani yimin wulak'anci bayan kuma na karb'i matar da kuka had'a baki kuka auramin...?" KHALEEL dake driven jin abunda BB ya fad'a yasa shi sakin baki da mamaki shimfid'e saman fuskarsa ya kashe wayan,sai da ya zo bakin get sannan ya kirashi,yana d'auka ya furta "Idan kaga dama ka iya fitowa mu wuce ko...?" Daga haka ko bai bashi damar yin magana ba ya kashe,bakin get en ya fito yana ganin motan babu magana ya bud'e ya shiga ba tare da ya kula shiba ya rufe k'ofan yana gintse fuska shi a dole ga wanda akama auren da baya so.Kallonsa KHALEEL yayi ya d'auke kai kamar ana fisgar maganar daga bakinsa ya furta "MR pretender ka gama yanzun....?" Kallon sa yayi cike da son tambayansa,gane hakan da KHALEEL yayi yasa ya furta "Ciwon SO mana...ba shi ya kwantar da kaiba ne...? ko an fad'a maka bamu san halin da kake ciki bane..?" "Allah ya sawak'e ciwon so kuma kamar wani mara abun yi zan kwanta ciwo kuma a hakama wai na so.." Dariya sosai KHALEEL yayi "Ehh! lallaifa ka samu lafiya tunda ka samu ABINDA RANKA KE SO ai dole kayi wannan maganar..Amma tunda hakane yanzun muje gurinsu ABBA kaga tunda baka son auren sai a warware tun tafiya bata yi nisa ba ko....?" Yamutsa fuska BB yayi sannan ya furta "Ka makara kuma ai dan ni a tsarina babu saki...Kuma ko bayan hakama ni yanzun ai na riga da na karb'a tunda babu yadda zanyi,ko ba haka nace maka ba...So no need kuma ace za a warware zanyi taimako..?" "Kutt!!! wai K'anwar tawa kake cewa zaka taimakawa...?" "Yeahhh! Itanfa.." "Haba MAN kaima da kanka kasan ta wuce haka wollahi kai dai kawai ta taimaka maka dan karka mace akan so,kama rufawa kanka asiri kayi shiru haka nan,dan kana ci gaba da magana zan nad'e komai na sanar mata,sannan kuma zan bata shawaran ta baka wahala ne ko me kazo da shi kada ta yarda..." Dariya sosai sukayi daga haka kuma BB ya canja musu firan..Haka har suka iso gidan iyayen nasu. Gidan a cike da jama'a y'an biki da basu k'arasa tafiya ba,bayan sun gama gaisawa da su,suka wuce babban parlor inda su ABBA suke tattaunawa da su OLD KHALEED da kuma KAKA da k'afarsa tayi kyau kamar ba shi yayi muguwar jinya ba.. Kowa yaga BB sai yayi dariya a cikinsu,shi dai kam bai iya cewa komaiba har sukayi shirin ficewa bayan sun gama gaishe-gaishen suka kama hanyan komawa gida,a hanya ne BB ya kalli KHALEEL yana fad'in "MAN nifa har yanzun ka sani a duhu wallahi kuma kak'i warwaremin yadda wannan al'amarin ya faru.." 'Dan murmushi yayi kafin yayi parking gefen hanya ya furta "Zaka iya tuna wata rana da muka je gurin UMMI akan maganar auren KHUBRA da nake sonyi a wancan lokacin...?" Kallonsa kawai BB yayi ya girgiza masa kai "Baka tuna ba ko..?" Nanma kai ya sake d'aga masa "Toh! idan baka mantaba kamar yadda na fara fad'a maka yanzun tun a wannan ranar dana jema da UMMI maganar wacce mukayi a gaban idonka,yanayin yadda kabar gidan shi ya bamu tsoro,a take UMMI tasa nabi bayanka amma ina fitowa na tarar har ka shiga mota wanda a k'ok'arinka na yin reverse har ka daki round about amma ko kulawa baka yi ba,in tak'ai ce maka zance har biyoka nayi a baya,sai da na tabbatar da ka isa gida lafiya sannan na koma,a nan na shaidawa UMMI duk abunda ya faru...Kasan abun da ya bani mamaki a lokacin? Bud'ar bakin UMMI bata furta komaiba sai cewa tayi KISHI ke damunka kuma ba kan komaiba ne sai kan wannan maganar da nayi mata,tun daga lokacin UMMI tayi ta bani baki akan nayi hak'uri da maganar KHUBRA,da tarin shawarwarin da take bani yasa na mata alk'awarin na janye neman auren,sai dai kuma abunda yasa bamu nuna a fili ba shi ne ganin yadda a fili kake nuna halin ko in kula da lamarin yarinyar bayan kuma a gefe kana fama da dakon soyayyarta,wannan dalilin yasa muka shirya maka wannan drama daka gani. A ranar d'aurin aurema nasan zaka ce to kuma me yasa aka fara sanar da d'aurin aure da sunana ko? to gaskiya wannan kuma ba daga mu bane daga mai sanarwar ne dan dama a yadda muka shirya mun barshi a kan sai a gurin d'aurin aure za kaji komai... Mistake en da aka samu yasa ka bar gurin ba tare da ka tsaya kaji d'aurin auren ba,wanda yanayin da na tarar da kai bayan gama d'aurin auren yasa nayi niyyan sanar maka da duk wani shirin da muka yi maka,sai dai kak'i saurarona,dalili kenan daya sa al'amura suka zo a haka...ina fatan yanzun ka fahimta..." Kallonsa kawai BB keyi fuskarsa d'auke da wasu irin expressions yama rasa me ya kamata ya sakawa da aminin nasa da shi,a hankali ya rik'o hannunsa sosai "Ban san da wane irin kalmomi ya kamata nayi maka godiyaba,kamin abunda ba zai tab'a gogewa daga zuciyata da rayuwataba,bani da bakin da zan iya gode maka,na gode na gode sosai d'an uwana...Allah ya baka mace ta gari wacce zata kula da kai.." Da sauri KHALEEL yana murmushi ya furta "Tabbas ya bani sai dai fatan Allah ya bamu zuri'a ta gari..." Sai da suka gama hiran yadda al'amura suka wakana sannan suka yi gaba,sai da ya sauke BB a gida kafin ya wuce nasa gidan. A parlor ya tadda su suna fama da kallon wani adventure film a MBC 2,nan ya zauna shima tun shigowansa da suka amsa sallama KHUBRA ko kallonsa bata sake yiba,har after asr prayer FATAHIYYA na gidan sai wajejen 5 sannan tayi niyyan tafiya gida. Driver'n daya kawo musu lunch shi ya dawo da dinner sannan suka tafi da FATAHIYYA,gidan yayi mata shiru babu abokiyar hira,sai BB dake kwance yana faman chat,ita dai bata da aikin daya wuce idan ta kalleshi ta tab'e baki ta kuma juya taci gaba da kallonta..Har bayan Maghreb suna a haka wajejen 10 kuwa suka sake sa wani film mai suna *DRAG ME TO HELL* film en abun tsoro musamman yadda a farkon film en inda ake marin iyayen yaron da malamar dake masa addu'a saboda yadda yake yi kamar mai iskokai,yadda aka cilloshi daga saman stairs bayan nan kuma k'asa ta bud'e wuta na ci ta ciki take kuma yaron ya nutse... KHUBRA dake wani cuition en daban,bata san lokacin data koma kusa da BB ba,yana chat lokacin yaji mutum a kusa da shi,kallonta kad'ai yayi yaci gaba da abunda yake yi,kallonta take ci gaba da yi idan taga abun tsoro saita sake shigewa jikinsa,shi kuma yak'i kulata dan bai sanma me ake a channel enba,maganar da suke da KHALEEL ya d'auke masa hankali kan maganar makaranta da yake ganin ya kamata ace an sa KHUBRA'N. Dai² gurin da yarinyar ta farka lokacin da wani k'waro ya shige mata hanci ta farka a bacci,har ta koma ta kwanta taji abu kusa da ita juyawan da za tayi tayi arba da wani irin halitta...Take ko suka kwala ihu tare da KHUBRA data gama cukuikuye BB,wanda ihunta yasa shi kallonta da kuma cikin parlor'n,TV en ya kalla take ya gano dalilin daya sata yin hakan,murmushi yayi yayi switching TV en,sannan ya mik'e da ita a jikinsa saboda yadda ta rik'e shi ya tabbata ba zata yadda ya kyaleta ita d'aya cikin parlor ba.... *~TEAM KHUBRA-KHALEED.~* *_.®єαl $mαѕhєr._* 😉 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/ *©®2018* *31/ʝųlყ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ 5⃣6⃣ *H* anyan bedroom enta ya nufa ita dai tayi luf a jikinsa,k'wak'warran motsi ta gagara yinsa bare yasa ran zasu rabu,sai da ya tabbatar da ya zaunar da ita a saman bed sannan ya mik'e da niyyan fita,hakan KHUBRA data gani shi yasata buga wani tsalle daga inda take,aiko nan ta rik'e shi cike da son tayi kuka ta fara magana "YAYA ina kuma zaka tafi...?" "Bedroom nawa zan wuce mana,wani abu ne ya faru kuma..?" Ya tambaya kamar bai san komai ba,kame-kame KHUBRA ta soma fuskarta cike da damuwa,duk wani abu da take idanunsa na kanta,shi kad'ai yake sakin murmushin mugunta,jira kad'ai yake tace ba zata iya zama nanba,ai ko take ya jiyota tana fad'in "Dan Allah YAYA ka tsaya a nan,baran iya zama ni kad'aiba kaji...?" Idanunta duk sunyi rau-rau wanda k'iris take jira ta fashe masa da kuka,a hankali ya fara magana "A'a BABY ni kuma nawa d'akin waye ne zai kwana ciki...Ki kwanta kinji babu abunda zai faru,kinga jiyama na tsaya inda kike saboda na tarar dake baki jin dad'i...kinga yau kuma tunda kinji sauk'i saina tafi nawa room en ko...?" Hakan daya fad'a shiya jawo hawaye suka fara tsere a saman fuskarta,cikin sheshshek'ar kuka take magana "Dan Allah YAYANAH kaji kagafa ina jin tsoron wannan abun na can..." "Haba mana BABY idan kikayi addu'ah babu abunda zai sameki kinji ko,maza je kiyi wanka ina jiranki kafin nan sai na wuce..." "A'a wollahi ni bazan iya shigaba ni kad'ai sai dai ka rakani....Dan Allah YAYA kaji zaka kwana a nan...?" Shiru yayi yana kallonta har lokacin kuma hawayen basu daina zubowa daga idanuntaba "Lallai ashe haka take da d'an banzan tsoro...? in dai kuwa haka ne to tabbas babu wata wahala da zai sha gurin shawo kanta.." Hannunsa ta dad'a k'ank'amewa jin yayi shiru bai ce komaiba while her eyes continuously shading tears,a hankali ya d'an kalli yadda ta cukuikuyeshi sannan ya d'aga mata kai yana fad'in "Ehmmm! muje dai kiyi wanka tukuna sai muyi maganar latter.." 'Dan murmushi ta saki,da kansa ya goge mata face nata sannan yaja hannunta zuwa toilet,ko da suka shiga bayan ya rakata yana k'ok'arin fitowa nan fa KHUBRA ta kafe akan itafa lallai sai dai ya jirata nan cikin toilet,rarrashi babu irin wanda bai mata ba akan ta hak'ura ya jirata cikin room en amma ina sam tak'i amincewa "Ni kam BABY ban san me kuma kike so nayi mikiba..Nace zan jira ki fito.." "Ni dai gaskiya a'a idan baraka tsaya ni nanba Allah zan fasa wanka'n ma gaba d'aya.." Cikin zuciyarsa yake fad'in "lallai na had'u da rigima,banda abunta ta ina zan iya jiranta a nan...?" "YAYA nifa tsoro nike kada su biyoni nan..." "To banda abunki ai canma zaki na ganina ba sai na tsaya nanba..kiyi wankanki babu abunda zai sameki ko ina nan ko bana nan.." Yana fad'in haka ya juya zai fice,take ta doka tsalle ta mak'alk'ale shi tana sakin sabon kuka "Allah kuwan nama fasa wankan gaba d'aya..Shi kenan dan bani da kowa sai kace zaka barni nan salon suzo su d'auke ni nima..Kuma Allah saina fad'awa ABBA su zo su maidani gida tunda haka ne..." Sake baki yayi yana kallon sabon salon tab'aran nata,komai nata cike da yarinta take yinsa,shi kam bai san kuma ya zai mataba,amma kam tabbas bai iya jiranta cikin toilet en kome za tayi kuwa.A kaikaice ya kalleta har lokacin tana faman matse idanu,fuskarta duk ta sauya tayi ja saboda azabar kuka data sama ranta fitina. "Haba mana duk abun bai kai nanba ta ina zaki fad'awa ABBA akan wannan d'an maganar shi ne zaki kai musu k'arana....?" "To ba kaine kace baraka jiraniba nayi wankan.." "Haba mana sai kace k'aramar yarinya zakiyi wanka gabana ko baki jin kunya tane...?" "Ina ji amma wollahi baran iya zama ni kad'ai cikiba...Sai dai ka zauna ka jirani..." "Lallai BABY kina da rigima ta ina namiji kamata zan tsaya kallonki kina wanka a gabana...Da sake wollahi 'wai an bawa mai kaza kai' idan kuma bani kike so nayi miki wankan ba to kam ya zama tilas ki kyaleni nayi waje..." "Tabbbbb! Allah ya sawak'e ta ina zan wani tsaya k'ato da kai ka wani yimin wanka,yo to ko ina jinya ai bakamin wankaba,k'arshe kam sai dai wollahi a bari idan na samu sauk'i nayi...Gara nayita zama da datti..." Bud'e baki yayi yana kallon yadda take zuba mishi fitsara,harda su murgud'a masa bakii,hannunta dake sak'ale da nasa ya dank'a sosai har sai da tayi y'ar k'ara "Ba dai kin iya fitsara ba,zan gyara miki zama soon....Kin ce ko kina jinya babu maiyi miki wanka ko...?" "Eh en to da akwai ne...?" Murmushi ya saki ganin har lokacin bakinta yak'i mutuwa,duk da irin yadda ta rintse idanunta kan zafin rik'on da yayi mata "Oyaahh! sake min hannu na fice wanka kuma kada kiyi,ki fito haka nan kiga yadda zanyi dake..." "Allah baran sake maka hannu ba...sai ka jirani tukuna.." "Kin san Allah idan baki sake mun hannuba zan miki abunda baki tunani yanzun..." Tab'e fuskanta ta sakeyi tana sakin kuka,cikin muryan kukan kuma take fad'in "Allah sai dai kayi koma mene amma kam ban sakinka yau...Salon ina wanka kawai su zo su d'auke ni,ni wollahi a'a babu inda zaka..." Murmushin mugunta ya saki,kafin tayi wani k'wak'waran motsi ya sureta bai direta ko inaba sai cikin bath tube,duk mutsu-mutsunta da ihun da take masa akan ya kyaleta bai sauraretaba sai daya rabata da kaf kayan jikinta fuskarsa a d'aure yake magana "Kin tsaya ko kuwa saina mareki ban fad'a miki kiyi wankan da kanki ba kika k'i...?" "Wayyoo! MAMA dan Allah ka kyaleni zanyi na yadda ka fita wajen zanyi da kaina,dan Allah kada ka kalleni ka rufe idonka..." Duk maganar da take idanunta a rufe suke hannayenta a saman chest nata tana k'ok'arin rufe jikinta..Ko ta kanta baibiba saima hannunta daya ke k'ok'arin b'amb'arewa daga inda ta musu matsuguni duk da babu abunda suka rufe daga jikinta da take son b'oyewa. Baki ya tab'e suna kuma ci gaba da kokawa da ita akan abunda yake niyyan yi. "Kin san Allah...." Kafin ya k'arasa ta bashi amsa "Da ce maka akayi ban sa shi ba..." Da mamaki ya kalleta "Lallai wato bakinki bazai mutuba ko...?" "To dama ance maka zai mutu ne ai shi da mutuwa sai ranar dana daina numfashiiiiiii....." Kafin k'arasa bashi amsan yasa yatsansa ya d'alle mata bakin fitsaran "Saboda kin raina ni yasa ina magana kina bani amsa ko kuwa...? Shiru tayi tana murza bakinta dayake mata zafi coz taji shigan abunda ya mata,baki ta kyab'e za tayi masa kuka "Kin min shiru ko saina k'ara miki wani...Duk ranar da nayi magana kika sake bani amsa makamanciyar wannan Allah sai nayi maganinki.." "Nifa ba wani abu nace ba..." "Kin min shiru ko kuwa...? Na tambayeki ne da zakiyi magana...?" Bakinta ta kame tana k'unk'uni k'asa-k'asa wanda sautin magana sam baya fita "Zagina kike yi ko..?" Idonta ta bud'e da sauri ta marairaice fuska "Allah ya baka hak'uri ni ba zaginka nayiba fa...amm! dan Allah YAYANAH kaji ka bari zanyi da kaina..." Wani mugun kallo ya watsa mata yana fad'in "Ina wasa dake ne kam..?" Kai ta girgiza masa "Idan na sake jin bakinki akan wannan maganar Allah zan sab'a miki.." 'Dif tayi ta maida idonta ta kulle,tana ji tana gani haka ya shiga dirzarta yanayi yana kallon fuskanta yaga ko ta bud'e idon amma still suna kulle sai chest enta dake harbawa da sauri-sauri,wankan da baifi 15 minutes ba sai da aka b'ata sama da one hour ana abu d'aya guri d'aya kawai yake wankewa idanunsa tsaye kyam a guri guda ya kasa kauda su,gajiya tayi dan da farko dama cewa tayi barata sake magana ba,ganin abun nasa ba na k'are bane ta furta "YAYA nifa na gaji wannan wankan yak'i k'arewa kamar an kawo maka y'an matan duniya ka wanke.." Murmushi yayi shi kad'ai kuma ya furta "An kusa gamawa ai..." "Tabbb! inafa aka kusa abu da har yanzu a gurin...." Bakinta tayi saurin dasawa pad lock jin b'aramb'aramar da take shirin yi. "Kin ce mene...?" "A'a fa babu komai...Dama ina son cewa bacci nake ji ne.." "Ohh! na zata suma kike ji ai,ashe a bacci kad'ai aka tsaya...da kinyi da kanki ai baraki jima haka ba...Ko da yake dama haka kike so ai tunda nayi miki da kaina shi kenan hankalinki ya kwanta..." Haushin maganarsa taji sosai dan tsabar wulak'anci ita zai kalla ya fad'awa haka...amma saita gimtse ta fasa magana saboda kada ta jawowa kanta wani abun dan kam bata manta d'alle mata baki da yayiba d'azun ba jimawa. Da k'yar ta samu Allah dai ya taimaketa ya d'auraye mata kumfan ya nad'eta a towel,d'aukota yayi ya fito da ita,a kan bed ya direta yana fad'in "Ki jira na fito yanzun.." "YAYA ina kuma za kaje to...?" A kaikaice ya kalleta yanafad'in "Zanyi wanka ne yanzun ina fitowa" "Wayyoo! Allah na dan Allah YAYA ka tafi dani wollahi ni tsoro nake ji..Baran iya zama nan ni d'aya ba.." Kallon ta kawai ya tsaya yi,lallaima yarinyar nan tana son jefa shi cikin bala'i idan ba neman fitinaba irin nata ta yaya zai tafi da ita cikin toilet,bayan tarin fitinar data ke neman jefashi wanda ba don ya kai zuciyarsa nesaba da yanzun a toilet tuni labarin ya canja salo.A fili kuwa sai cewa yayi "A'a ki dai jirani nan zan bar miki door en a bud'e shi kenan..?" "Aaaaa! ni dai a'a gaskiya.." Fuska ya had'e yana kallonta cikin alaman kamar ransa ya d'an soma b'aci yace "Shi kenan ai sai ki taso,amma kam ki tabbata idan har k'afarki ta taka cikin toilet ennan to ina mai tabbatar miki da sai dai kiyi min wankan...Zab'i ya rage naki ko ki zauna nan ko ki bini ki kuma yimin duk abunda nasa ki.." Da sauri ta kalleshi tana komawa tana zama,gira ya d'age mata yana fad'in "Yesss! haka nake nufi,zaki bini har yanzun...?" Da sauri ta kad'a masa kai alamar a'a,shiko murmushi yayi a zuciyarsa yana fad'in "Da kin ce eh ai da kuwa kinga d'anyen kai" A fili kuma ya furta "Kin ceci kanki yarinya.." Ita dai kanta nak'asa har ya bar gurin ya shige toilet a yayin da ya bar k'ofan a bud'e tana jiyo motsinsa.Tagumi ta buga idanunta na kan door en har ya gama abunda yake ya fito d'aure da towel,d'agowa tayi ta kalleshi ganinsa daga shi sai towel yasa tayi yin ihu,da sauri ya iso ya rik'e shoulders enta yana fad'in "Lafiya kikema mutane ihu da daren nan..?" "Ni kasa kayanka ka wani fitowa mutane a haka.." Wani uban tsaki ya ja shi a tunaninsa bai kawoma abunda yasa take ihu ba kenan,amma ya ya iya da wannan shugabar rigimar tasa,kan dole ya lallab'ata tayi masa shiru amma ta dage sai ya tashi ya sa kaya,sai daya juya mata baya sannan ya fara magana "Ke wollahi ban tab'a ganin mutum mai rigima irin kiba,sai kace ke ba towel en ne a jikinki ba zaki dasa ma mutane rikici da wannan daren.." Bata kula shi ba har ya gama maganarsa shi kad'ai coz a lokacin ma abunda ya hanata tanka masa saboda kada ya korata nata d'akin,ita kuma tsoro bazai barta ta iya kwanciya ita d'aya ba.Har nata bedroom en ya rakata ta d'auka abunda take buk'ata sannan suka dawo tare,yana kwance saman bed yana fama da waya ita kuma ta juya a nan ta shirya cikin riga dogo mai laushi turarukansa ta feshe jikinta dasu dan ba abunda zai sata fita yanzun,har ta gama ta hauro saman bed en daga gefensa ta kwanta,da sauri ya kalleta yana matsawa gefe "Heyy! MADAM da fatan dai ba nan zaki kwantaba ko..?" Marairaicewa tayi kamar za tayi kuka "YAYA toh ina zan kwanta..?" "Can zaki koma a can zaki kwanta.." Ya mata nuni da cuition dake can gefe,da sauri ta kalleshi kamar za tayi kuka tana fad'in "Dan Allah kayi hak'uri wollahi baran iya kwanciya canba,kaga ina jin tsoro sosai..Dan Allah kaji.." Dad'a d'aure fuska yayi yana magana like serious "Kinga MALAMA gara dai kiyi nesa da ni,ni babu abunda zaisa na kwana tare da ke a guri d'aya." Kuka sosai tasa masa tana ta faman begging ensa,juya mata baya yayi alamar babu wasa a cikin maganarsa ita kuma tak'i dainawa,a hankali ya juyo yana fad'in "Ok! shi kenan an gama ya isa haka kukan.... Shugabar masu kula ta duniya... Idan kin yaddafa amma ko ina da sharad'i.." Da sauri ta matso tsakiyan bed en tana fad'in "Allah na yarda koma mene ne ba zan maka musuba kaji.." "Kin tabbata...?" Nanma ta sake d'aga masa kai da eh "Ok c'mon..." Da sauri ta shige jikinsa ganin yadda ya bud'e mata hannu,hannunsa ya mayar ya rufe,yana sauke wani wawan ajiyan zuciya,a kunnenta ya rad'a mata "Kin ce kin amince da sharad'ina ko..?" Kai ta sake girgizawa "Ok...! Duk abunda kikaga nayi ban son magana,kin gane ko..?" Again ta sake girgiza masa kai Daga haka bai sake magana ba yayi musu addu'ah,ita dai KHUBRA tana kwance jikinsa babu damuwan ko wani abu da zai je ya dawo,yayin da a b'angaren BB jinta a karo na biyu a cikin jikinsa jiyoyin sha'awa suka fara motsawa,a hanakli ya fara shafa bayanta yana dad'a shinshinar jikinta.Cikin alamun bacci ta ce "YAYA ka bari nifa bacci nike ji.." A kunnenta ya rad'a mata "Baran iyaba BABY ba na fad'a miki ban son magana ba.?" "To ni ka kyaleni na ce banso dai ko..?" Tana maganar tana kuma ture hannunsa dake yawo cikin riganta. Da k'yar ya iya bud'e idanunsa da suka masa nauyi baya ga colour da suka soma sauyawa.Tuna yadda suka yi yasa ya mirgina gefe yana fad'in "Ok! tunda baki so maza tashi ki koma d'akin ki..." Jin haka yasa ta tuno yadda yarinyar film en ke shan wahala da sauri ko ta furta "A'a a'a! na yarda.....Amma dai dan Allah YAYA ka bari Allah babu dad'i abunda kakemin kaman tafiyar tsutsafa nake ji a jikina.." 'Dan murmushi ya sake dan yana ganin yadda take maganar "Ok...! tunda baki so ai na baki zab'i zaki iya komawa d'akinki.." "A'a ai na fasa tafiya baran iya kwana ni d'aya ba.." "Ok! toh zo nan.." Babu musu ta sake shigewa jikinsa,idanunta runtse kamar wani zai kamata,tana ji tana kuma gani yaci gaba da sarrafata son ransa................ *~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~* *_®єαl $mαѕhєr._* 😉 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/ *©®2018* *2/ɑմցմՏԵ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ 5⃣7⃣ *A* hankali cikin nutsuwa yake aika mata sak'onninsa wanda yasa lokaci guda jikinta yayi mugun sanyi,cikin dabara yake juyata side zuwa side,komai da yake yi yana yinsa ne cikin nutsuwa coz yana gudun kada su samu matsala. Soyayyarta game da tausayinta su suka narka masa zuciya wanda sune sinadarin da yasa yake lallab'ata tamkar tsoka d'aya a cikin miya,yanayin jikinta da kuma halittun da Allah ya wadatata dasu wanda ya sake yin tozali dasu su suka k'arasa rud'ashi game kuma da birkita masa lissafi,wad'anda sune sukayi jagora na rusa duk wani plan nasa na son ya bita a sannu,cikin zafi-zafi ya koma aika mata da sak'k'onninsa masu girma wanda suka sa KHUBRA kasa jurewa,da farko ta so ta musa ma buk'atarsa kamar yadda a farko tayima kanta alk'awarin bazata hana shi hak'k'insa ba da Allah ya d'ora mata,sai dai kuma yanayin y'an aikensa su suka sa ta bada kai bori ya hau.Cike da so da kuma k'auna wanda zuciyarsa ta kasa kiyasta adadin hakan a tare da ita,duk kuka da kiran da KHUBRA kewa y'an gida kan neman taimako babu abunda yasa BB ya d'aga mata k'afa face k'aimi da azama daya sake k'arawa na ganin ya cilla kwallonsa a raga,bayan komai ya lafa yana rungume da ita cikin jikinsa hawayenta har lokacin suna ci gaba da sauka saman chest nasa,da sauri ya mai data k'asa yasa hannunsa yayi cupping face nata,harshensa yasa yana d'auke mata duk wani hawaye dake biyo fuskan nata,cikin kunnenta kuma yana rad'a mata how he luv's her,ita kam KHUBRA a wannan lokacin damuwarta yadda jikinta ke mata azaba,amma kuma wani b'angare na zuciyarta,na tare da shi kalamansa na dad'a narka mata ilahirin gangar jíkíntα,sαí dαí kumα wαní bígírє dαgα zuciyarta na tunatar da ita girma da kuma lokacin data shafe da soyayyarsa data jima a mak'ale cikin zuciyarta tun a wancan lokacin na baya wanda duk ranar data tuna rabuwarta da shi ta k'arshe cikin mafarkinta dai dai tayi murmushi mai ciwo,sai gashi yanzun ta same shi a gaske tunanin da bai tab'a zuwa zuciyarta ba kenan murmushi tayi a lokacin mai cike da sukuni,idan har bata mantaba tun bayan zuwanta gidansu ZUHRA bata sake mafarki da shiba,a she a lokacin'ma suna kusa da juna,sam BB bai san mai ke gudana a tare da itaba a lokacin shi dai kam burinsa a lokacin bai wuce ya kafa gwamnatinsa ba duk kuwa da yanda yake da yak'inin kalamansa na tasiri a tare da ita,da sauri ta dawo duniyarta tana sauraren kalaman da suke mata yawo cikin jini da b'argo na jikinta,a wannan lokacin duk wata y'a mace da zata saurari kalaman dake fitowa daga bakin BB to tabbas babu makawa sai ta fad'a TARKON K'AUNA koda kuwa ace bata tab'a tsintar kanta cikin soyayya ba,halin da take tsintar kanta a wannan lokacin da BB yasan halin da yake jefa zuciyarta to da tabbas babu abunda zai sa bai k'ara k'aimi gurin ganin k'arasa narkar da ilahirin zuciyarta ba,ji take a lokacin inama tana da bakin magana to kuwa da tabbas babu abunda zai fito daga bakinta sai dai tace "Ya barshi haka nan tun kafin zuciya da gangar jikinta ya gama yin melting saboda girman kalaman da yake amfani dasu..." Sai dai kash babu bakin magana bare wannan kalamai su fito daga bakinta,haka taci gaba da saurarensa. Duk da ganin irin sa'ar da tayi a matsayinta na wacce tayi dace da salihin miji hakan ba zai hanata kukaba saboda ta gurzu a hannunsa,duk fitsara irin tata data ke ji da ita a lokacin kam tayi k'us babu baki sai kunne.Wani wawan ajiyan zuciya ta shiga saukewa akai-akai,tausayinta duk ya cika shi ganin irin halin da ya jefa abar k'aunar tasa,rarrashi kam ya shashi a cikin wannan dare mai cike da d'umbin alkhairai wad'anda baki ba zai iya lissafasuba. Kiraye-kirayen salla'n asubah shi yasa shi yunk'urin mik'ewa ya gyara mata kwanciyanta dan a lokacin kam tuni bacci yayi gaba da ita cike da wahala take baccin idanunta sun shige ciki saboda kumburi da suka yi,fuskarta ya shafa sannan ya ja mata duvet en ya rufeta,ya nufi hanyan toilet sai sakin murmushi yake shi kad'ai,sai daya tabbatar ya tsarkake jikinsa,ya kuma tanadi ruwa mai zafi irin wanda ba zai cutar da mutum ba,sannan ya dawo baccinta har yayi nisa,bai saurara mataba sai daya kaita har cikin bath tube,jinta cikin ruwan daya ratsata wani sabon azaba ya ziyarceta data ji shi from head to toe,take tayi wani uban zillo tana shirin fitowa,da sauri ya maidata ciki yana fad'in "Easy baby..." Sabon kuka tasa masa,murya dishii-dishi ta soma fad'in "Bayan tarin muguntar da kayi min bai isheka ba saika had'a da k'arasa ni....Wannan ma ai mugunta ne kawai ka kama kana wani dafani kamar ka samu ganda...kuma Allah sai ya sakamin kan muguntar da kamin.." Yana jinta sai murmushi yake yana kuma bata hak'uri dan yasan shi ne mai laifi.Cikin kuka take ci gaba da fad'in "Ai dole ka sani gaba kana bani hak'uri tunda kasan ka gama da ni,inba muguntaba ai sai dana ce maka ban so amma ka wani dage...harda wani cewa sharad'i ashe sharad'in mugunta ne bana komaiba..." Sai da yayi murmushi sannan ya sunkuya cikin kunnenta yake fad'in "Yanzunma ki gama min fitsaran ina da k'arin sharad'i..." "Wallahi a'a babu wani sharad'inka da zan sake saurara...haka kawai naje ka kashe ni..dan wollahi ina jin yanzu'nma bazan k'ara iya tafiya ba,shi kenan na zama gurguwa..." Tana fad'in haka ta sake kecewa da kuka harda sheshshek'a,dariya ya saki yana shafa bayanta,da sauri ta doke hannunsa dake yawo a bayanta cikin kuka take masa masifa "Ni ka bari bana so,ai dama da haka ka cuce ni d'azunma..." Zallan futsara take zuba masa,amma sam BB bai ga laifinta ba a lokacin coz yasan shi ya janyo wannan rikicin nata.Sai daya wanketa tas a karo na biyu sannan ya barta ta k'arasa,yana jinta duk magananun da take idanunta a kulle suke ta kasa had'a ido dashi,a nan jikin wall na toilet en ya tsaya jiranta dan kam yana da tabbacin wannan sarauniyar rakin bazata iya fitowaba tunma dama can ta fad'a masa kad'an ya rage mata ta zama gurguwa.Tunani ya fad'a yadda daren ya kasance a gare shi,murmushi kad'ai yake saki idanunsa rufe kamar mai bacci. Bayan ta gama tana k'ok'arin mik'ewa taji azabar data fi k'arfinta babu shiri ta koma ta zauna tana sakin kuka,cikin kuka take fad'in "Wayyooo! Allah na MAMA shi kenan na zama gurguwa,wayoo ni shi kenan baran sake tafiya ba..." Kukanta ne ya dawo da shi duniyarsa da sauri ya koma,baiyi mata magana ba ya d'auketa yayi waje da ita a kan bed ya direta ya juta ya fice a d'akin,bedroom enta ya isa kai tsaye ya d'auko mata jallabiyya da hijab ya dawo,shi da kansa ya sa mata sannan ya d'auketa ya dire a kan pray mat daya shimfid'a,fuska babu fara'a haka ta cunkushe ita a dole ga wacce akayiwa laifi,jam'i ya jasu raka'atanul fijr suka fara gabatarwa sannan suka sallacci asubah,ya d'an jima yana musu addu'a wanda sam bai kula da abunda KHUBRA keyiba,sai bayan daya k'are tukuna yana juyowa ya ganta kwance da alama kam baccinta take a lokacin d'an murmushi yayi sannan ya mik'e ya d'auke pray mat en,cak ya d'auketa a gurin ya maidata saman bed,sannan ya gyara mata kwanciya,kusa da ita ya haura ya kwanta tare da sata cikin jikinsa suka koma bacci.... 《《》》 Kulawa ta mussaman KHALEEL ke bawa ZUHRA wadda bata tab'a tunanin samunta daga kowa ba,cike da so da k'auna suke nunawa juna kulawa,kwanaki biyu da aurensu sun koma matsayin abu guda duk inda d'aya yake to tabbas zaka samu d'ayan a tare da shi.. B'angaren ASHNA da SADEEQ ma ba'a cewa komai dan kam soyayya ko wasu turawan sai dai su d'aga k'afa coz babu abunda zasu fisu,idan har ka shiga wannan gida to tabbas ba zaka so ka fito ba saboda soyayyarsu mai cike da burgewa da mutunta juna babu raini... 《《》》 Sai around 11:00am ta farka idanunta ta shiga bud'ewa a hankali har ta kammala bud'esu tas a kansa zaune kusa da k'afafunta,kallon da yake mata yasa tayi saurin mayar da su ta kulle saboda tabbas kam baza ta iya bud'esu ba matuk'ar yana gurin,d'an murmushi yayi ya dawo kusa da ita,hannunta ya rik'o cikin nasa,sai da yayi kissing hannun sannan ya d'ora fuskarsa akai,tana jinsa tayi masa banza dan kam tana jin haushinsa har yanzun,ga kuma nauyin bud'e idonta da take gabansa gudun kada su sake had'a ido da shi. Tunanin maganganunsa ta soma yi na jiya da yaketa faman rera mata acikin kunnenta,ita kad'ai take zancen zuci tana fad'in _"Uhmmm! KHUBRA kenan ke yanzun kuma har kin yarda da abunda ya fad'a...? ko kuwa kin manta gurzar daya miki kamar ya samu kayan wanki da sukayi uban datti,ji fa irin wahalar daya baki,idan har da yana sonki ne kamar yadda ya fad'a to da lallai babu abunda zaisa ya miki irin wannan muguntar,kawai ki share duk wani abu da zai fad'a miki...dai dai me kina ganin kamar kalamansa gaskiya ne a gareki ko ko din kina sonsa ne yasa kike tunanin gaskiya ya fad'a miki...?_ D'an k'aramin tsaki ta jaa,dai-dai lokacin wayanta dake saman mirror ya fara kuka,shi da kansa ya d'auko mata wayan ganin mai kiran nata yasa yayi murmushi yana fad'in "Ga CWEETY'NKI nan tana kiranki.." Hannu ta mik'a masa nan ya d'ora mata wayan kan hannunta tare da jan hancinta,d'an k'aramin k'ara tayi duk da yanayin muryanta da baya fita "Wayyoo! Allah YAYA zaka ciremin hancifa.." Y'ar dariya yayi mai sauti yana fad'in "Ko na cirema ai nawa ne ko..?" "A'a naka ai gashi nan a fuskanka.." "Ohhh! ba nawa bane kenan kike nufi ko mene...?" "Ehh mana naka ai yana kan fuskanka ma.." "Ohh! kina nufin abunki ba nawa bane ko..?" "Ehh en inda naka ne ai da bakamin abunda kayiminba da dare..." Murmushi ya sake yi mai sauti dai-dai fuskarta ya sunkuya yana fad'in "Ki gama gayamin magana son ranki anjima na kamaki sai nayi miki fiye da haka...Kin san wani abuma kuwa...to bazan barki kiyi bacci ba yau,kwana zamuyi ina sauke miki gajiyan dake jikinki...Kin gane ko..?" "Tabbb wollahi ba dani kake ba,sai kace wata inji..." Da sauri ta toshe bakinta,tana dad'a k'udundunewa cikin duvet,sanin babu komai jikinta daga ita sai towel,shima gaba d'aya ya gama nad'ewa zuwa can saman cinyoyinta wanda kad'an ya rage aga komai na daga halittanta. Bata ankaraba taji ya d'age duvet en,ihu ta saki tana k'ok'arin ja shima yana ja,kukan shagwab'a tasa masa tana fad'in "Dan Allah YAYA ka bari kagafa babu komai jikina..." "Ehh dama ai banson ganinki da komai,yanzunma ina son checking enki ne naga babu matsala...." Dai-dai kunnenta ya rad'a mata cikin murya da yake kashe jikin mai sauraro "Kinga dole na dubaki saboda anjima da dare bana son wani abu yamin shamaki daga d'and'anon zumanki..." Hannu tasa ta rufe kunnenta duka shi kuma ya fice yana mata dariya,da kyar ta bud'e idanunta sai lokacinma ta tuna da ZUHRA ta kirata bata d'aukaba ta biye masa,tana dubawa ko taga cikin rashin sani ashe ta d'auka daga can gefen da aka ji batayi maganaba aka kashe,har fiye da mintuna uku,da sauri ta dafe kai a fili take fad'in "Wayyoo Allah na Allah yasa baki ji komai ba" Kiranta ta shiga yi cikin shak'iyanci ZUHRA take fad'in "Amarya bakya laifi....ko da kin kashe d'an masu gida.." Cike da tsiwa KHUBRA ta tari numfashinta tana fad'in "Ai wollahi babu abunda zaki fad'amin...Yanzun ace harda had'in bakinki acikin wannan abun dake faruwa,ko ba komai ai na wuce haka a gurinki,amma shi ne kin san wannan maganar kiyi min shiru...babu komai na gode tunda kin san BB'N naki ba sona yake ba Amma kika wani yi shiru aka had'ani da shi,shi kuma YAH KHALEEL dama yaudarana yake ban saniba ashe.." "A'a CWEETY kada kiyi saurin yanke hukunci kan abunda baki saniba,ki bari kiji komai da yadda al'amura suka wakana,na tabbata ke da kanki zaki fuskanci abubuwan da suka faru a baya..." A tak'aice ta bawa KHUBRA labarin yadda BB ke sonta tunma kafin a saceta,har zuwa yadda aka shirya komai duk dan asa shi ya fito fili ya nuna da kansa,amma abu yaci tura,wanda daga k'arshe kuma hakan ya kaishi ga fad'awa mummunan yanayi,idonta ta runtse cike da tausayin irin halin da ya shiga akanta,ashe dama akwai lokacin da zata samu wanda zai sota har haka? ita kam ta tabbatar dalilin daya sata sakin jiki da shi a kwanakin nan ba komai bane illah tsoron fad'awa fushin ubangiji da kuma tsinuwar mala'iku,dalili kenan daya sata take k'ok'arin dasama zuciyarta soyayyarsa ko ta wane hali,sai gashi ta tsinci dami a akala,shi tunima ya gama macewa a soyayyarta Wanda bata saniba sai yanzun,lallai ko babu abunda zata yi masa a wannan hali face biyayya sau da k'afa... Hawayen da suka biyo fuskarta ta shiga gogewa dai-dai ZUHRA na mata tsiyar hiran da suke d'azun da BB,sai gashi ya dawo hannunsa d'auke da d'an k'aramin tray samansa kuma thick tea ne da toasted bread,hangota tana goge fuska hannunta dafe da phone enta dake jikin kunnenta har lokacin ya tabbatar da kuka take,da sauri ya k'araso wayan ya zare daga hannunta yakai kunnensa yana fad'in "Heyy! MADAM me kika fad'awa matata take kuka cikin wannan safiyar...? idan kinsan kuka zaki dunga samin ita idan kin kirata to a hak'ura da kiran kin gane ko...?" Yana gama fad'an abunda ke bakinsa ya kashe dai-dai lokacin kuma yana zama kusa da ita,d'agota yayi ya jinginata a jikinsa,dad'a narkewa tayi a jikinsa tana fashewa da sabon kuka,kansa ya dafe yana fad'in "Ya salaam..!" patting bayanta ya shiga yi,yana hura mata iska cikin kunnenta,nan da nan tayi shiru jin gaba d'aya vains nata sun soma saki,ta koma sakin ajiyar zuciya "Watoo abunda ta kira tamin kenan..ta saminke kuka hankalinta ya kwanta,zan gamu da ita tabbas sai na sab'a mata..." Da sauri ta rufe masa baki da hannunta tana girgiza masa kai cikin sanyi take fad'in "A'a YAYANAH...ko kad'an kada ka mata haka..ni nasan ba dan haka tayi ba,sai dan wata manufa ta daban...ko kad'an ba abunda kake tunani bane,dalilin kukana ba yana nufin abunda ta kira tayi ba kenan,hasalima ta kirani ne dan ta sanar dani wani muhimmin sak'o da ni kaina ban san dashiba... Kayi hak'uri YAYANAH sam ban san abunda ya faruba kenan,kuma ko da wasa babu wanda ya sanar dani,ina...ina...so...so..n...ka...nima fiye da yadda kake tunani...tun tasowata na rayune da soyayyarka,da ita na girma..tun ban san kaina ba har nazo na mallaki hankali..sai dai ko kad'an ban tab'a nunawa kowaba,gudun abunda zai faru.." Shiru tayi tana maida numfashi d'aya da d'aya,matar dake kunyar bud'e ido ta kalleshi sai gata idanunta cikin nasa tana falassa asirin zuciyarta.. Mamakin kalamanta yake sosai saboda baiyi tunanin faruwar hakanba,sai gashi tana sanar masa da soyayyarsa ta rayu..Yana tunanin ta katse shi dai-dai lokacin data ci gaba da fad'in "A lokacin da nake rayuwa cikin k'unci da tsanani soyayyarka ce kad'ai abunda ke k'aramin k'arfin guiwar ci gaba da rayuwa,badan hakaba da tabbas ban kawo yanzu'n ba,a lokacin da bani da kowa bani da komai sai zallar soyayyarka dake gudu cikin jinina,bana tare da kowa nawa amma idan na tuna da soyayyarka sai naji na zama mai cikakken gata,ina jina a matsayin wacce take da kowa...Dan Allah YAYANAH kaci gaba da sona har k'arshen numfashi,kada ka nunamin halin maza..." Ta k'arasa tana sake rungumeshi had'e da sakin sabon kuka mai tsuma zuciya,gaba d'aya ilahirin jikinsa ya saki jin irin maganganun dake fitowa daga bakinta kamar a mafarki,komai sai zuwa masa yake da sauk'i ba kamar yadda yayi tunaniba,ajiyan zuciya yayi yana fad'in "It's ok baby me,bana son kukan nan naki,ina jinsa ne har k'asan zuciyana..." Da sauri ta shiga gogewa tana girgiza masa kai had'e da murmushi mai burgewa.Murmushin shima ya saki yana janyo tray en dake kan bedside drower,babu musu ya shiga bata tana amsa,sai dai kuma fuskarta da take yamutsawa kamar mai had'iyan magani,duk wani abu da tayi shi kam burgeshi take had'e kuma da k'ara masa kyau.Duk duniya babu abunda yake so sama da ita,tausayi da kuma soyayyanta da suke dad'a taso masa daga can k'asan zuciyarsa su suke dad'a tasiri a lokacin a kansa. A haka har ya gama bata tea en da toasted bread,murmushi tayi masa tana shafa gefen fuskarsa ta furta "Na gode YAYANAH..." Hannunsa yasa saman bakinta ya rufe yana girgiza mata kai,cikin sanyin murya ya furta mata "Babu godiya acikin abunda ya zama wajibina..." Har ya mik'e zai fita ya juyo yana fad'in "Baby get ready idan na dawo zan miki wanka...." Ta gane dalilin da yasa ya fad'i haka duba da yadda ya mata winking,fuskarta tayi saurin b'oyewa,cikin sauri ya fice da tray en a hannunsa yana dariya,itama dariya tayi tana jin zuciyarta wasai,dawowarsa cikin d'akin tayi saurin b'oyewa cikin duvet har kanta tana tuna abunda zai mata yanzun kuma dan kam ta tabbata sai ya aikata abunda ya fad'a "Ehheem! MR'S KHALEED SAFWAN kin shirya ko kuwa yanzunma babu k'aton da zai miki wankan...?" Dariya tayi mai sauti tana fad'in "Ehhh! babu..." Kafin ta k'arasa ya sureta yayi hanyan toilet yana fad'in "Haba yarinya....zancen babu wani k'ato da zai miki wankama ai bai tasoba,tunda anyi abunda yafi wanka ko....?" B'oye fuskarta tayi cikin jikinsa sukayi dariya dukansu.ko a toilet enma shiriritarsu suka tsaya yi,sai da suka b'ata lokaci a ciki ana gumurzu tsakaninta da BB,shi yana wani aikin daban ita kuma tana masa raki haka suka fito,sai daifa akwai tarin tambayoyi a zuciyar BB da yake son yi mata kan maganarta na d'azun................... *COMMENT FOR MORE PAGE'S.........* 💃💃💃💃💃💃 *~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~* *_®єαl $mαѕhєr._* 😉 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/ *©®2018* *3/ɑմցմՏԵ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ 5⃣8⃣ *K* o bayan da suka fito daga wankan tsokanarta yayi tayi,burinsa bai wuce ta dad'a sakin jiki da shi sosai ,suyi rayuwa mai cike da tsafta da k'aunar juna cikin ko wane hali zasu kasance,duk yadda ta sanar da shi irin son da take masa tunma kafin wannan lokacin,amma kuma yana da burin jin labarin yadda ta rayu da soyayyarsa a lokacin da basu tab'a tozali da junan suba,cikin dabara ya shiryata sannan ya shirya kansa,kamar jaririya haka ta zame masa shi kuma duk abunda take yi ko kad'an bai ganin laifinta bare ya damu hasalima burgeshi take. Parlour suka fito tana jikinsa a lafe kamar mage,dama KHUBRA ba baya bace gurin son jiki yanzun kuma ta samu shi yasa ta dad'a manne masa,cikin kunnenta yake rad'a mata "Baby baki bani labarin yadda kika rayu da soyayyana ba kamar yadda kika fad'a.." Idanunta a rufe tana kwance kan chest ensa,tana ta faman zuba murmushi,abunda ya fad'a yasa ta sake duk'unk'unewa a jikinsa tana fad'in "Nima ai baka fad'amin labarin soyayyana ba.." Murmushi yayi mai sauti sannan ya d'ago fuskarta "Kina son ji ne...?" Kai ta d'aga masa,cikin zolaya yace "Oyyahhh! idan kina son na baki labari sai kin kalleni tukun kuma yanzun.." Dad'a sinne kai tayi a jikinsa tana fad'in "Tabbb! wollahi a'a ban iyawa.." "Shi kenan to tunda bakya son labarin sai a hak'ura" Da sauri ta katse shi tana fad'in "A'a a'a ni ka bani a haka,so kake kasa nayi ta jin kunyarka kenanma ko...?" "A'a ta yaya zan saki jin kunya,ni da nake sonma ki dena jin kunyana gaba d'aya.." "Ehhh! ammafa cewa kayi saina wani kalleka sannan zaka fad'amin.." Murmushi yayi yana k'ara rungumeta tsam a jikinsa,zuciyarsa kan tsananin farin cikin da yake ciki ji yake kamar ya ciro ya bata ita kyauta ko ya samu sassaucin tsananin soyayyan dake cin jikinsa,duk da kasancewar a yanzun gashi ga ta "Ok..! bari na baki labarin yanzun,amma da sharad'ifa..." Ya k'arasa yana dariya "Tabbb! ai na fad'a maka wollahi babu wani sharad'i da zan kuma yarda da shi indai naka ne.." Dariya yayi sosai har hak'oransa suna bayyana,sannan ya fara bata labarin irin son da yake mata tun daga ranar da suka dawo gida shi da KHALEEL zuwa lokacin farkon da KHALEEL ya nuna yana sonta,da halin daya shiga akanta bayan b'acewarta,zuwa lokacin da suka had'u da ita a k'auyen ZAKIRAI da kuma dawowarta har kawo yanzun da suke tare manne da juna. Ajiyan zuciya ta saki tana fad'in "Dank'ari..! Amma kumafa YAYANAH kasan wani abu,Allah gani nake nafika shan wahala akan soyayyan nan,ni abunda yayi saura da zan iya cewa bai same niba,shi ne rashin lafiya amma kam daf nake da kamuwa da ciwon zuciya musammanma lokacin da aka sa ranar aurena da YAH KHALEEL,Allah ko jina nake a lokacin kamar bana raye,gani nake kamar na koma mutum-mutumi saboda a lokacin nikam gani nake shi kenan na rasaka a rayuwata... Sai gashi na tsinci dami a akala,abunda sam ban kawowa zuciyata zai faruba sai gashi kamar a mafarki komai ya canja cikin lokaci kad'an.." "Hakane baby amma kumafa ba zakimin wayoba sai kin bani labarin yadda komai ya faru.." Murmushi tayi tana fad'in "Yanzun kuwa zan fad'a maka komai.." Nan itama ta shiga bashi labarin tun daga mafarkinta na farko da shi wanda ya janyo mata shan ruwa a gurin LADIYO data juye mata randa guda na ruwa akan batayi aikin data sata ba ta kwanta,k'arshe kuma dad'in mafarki yasa har bata ji lokacin da take rafka mata kiraba,daga nan ta d'ora masa da farkon zuwanta garin KANO zuwa rayuwarta a gidan MA'U da yadda mafarkinsa yayi ta jawo mata karb'ar na jaki a gurin MA'U har ta kai ga ta ture MA'U'N wata rana dalilin daya janyo mata targad'e kenan.Nan ta dakata tuna irin dariyar muguntar da tayi mata a ranar,dariya tayi a lokacin mai cike da sukuni na samun y'anci,hancinta ya lakace yana fad'in "Jodi wato kema kin iya dariyan mugunta ko...?" Kallonsa tayi tana murmushi jin ya kirata da wani suna na daban "Uhmm! Allah ko YAYANAH ko kai da kana gurin sai kayi mata dariya,musamman yadda take tafiya kamar wata...." Shiru tayi tana murmushi,a zuciyarta tace "Allah yaso ban k'arasa ba,dan ko ni nasan abunda naji da dare,garama da ban k'arasa ba.." Muryarsa ta tsinkayo yana fad'in "Nikam babu dariyan da zanyi,dan a lokaci'nma da ina da dama to da tabbas k'ara mata zanyi.." "Me yasa YAYANAH..?" Sai daya runtse idonsa coz gani yake kamar a lokacin abunda ta fad'a suke faruwa,cikin dashewar murya na mutumin dake cike da tausayi ya furta "Saboda ta wahalarmin abunda nafi k'auna a rayuwata..." Fuskarsa ta shafa tana murmushi "Yanzun kuma fa...Ai gani a kusa da kai ko.." "Haka ne mafi kusama kuwa...Tunda gaki kwance cikin jikina ba.. Ammafa duk da haka saina hukunta su saboda sun aikata laifi mafi girma a gareki..." "Ni kam YAYANAH bana son d'aukan wani mataki da zakayi,ina tunanin idan muka barsu da Allah zai isarmana,kuma ko bayan haka ma,tun yanzun kam ai sun fara girban abunda suka shuka..." "Haka ne jodi Allah ya mana maganin irinsu.." "Ameen YAYANAH..." "Emmm! ina binki bashi fa..." Kallonsa tayi da alamun neman k'arin bayani akan fuskarta "Ehh! mana.....ko kin manta ne? ai da sauran labarin dan baki gama ba ina kuma sauraronki..." "Kaiii YAYANAH kana da son labari.." "Ehh! naji amma labarin ba kowanne ba" "To sai wane iri..?" "Irin wannan mana da kike bani yanzun,ai shi nafi so na kuma fi buk'ata.." Ci gaba tayi da bashi labarin yadda ta gano shi ne mutumin mafarkinta har sai data k'are,kiss ya manna mata a porehead enta cikin sanyi ya furta "Da ace inada damar maida hannun agogo baya to da tabbas nayi hakan dan na samu daman goge duk wani tabo daya shafeki a rayuwa,sai dai kash babu halin yin haka...Amma yanzunma bata b'aciba zan kasance miki matsayin miji wanda zai baki dukkan wata kariya ta ganin babu abunda zai kuma samunki a gaba.." Tsam suka dad'a rungume junansu cike da soyayya da kulawa..Haka rayuwarsu taci gaba da tafiya cike da bawa junansu kulawa ta musamman. *TWO WEEK'S LEAP.* Kimanin sati biyu kenan da aurensu,har yau BB ko k'ofar gida bai sake koda fita ba,hasalima wayoyinsa gaba d'aya ya kashesu dan kawai kada a takura musu,a cewarsa amarci suke saboda haka babu mai damunsa. Yau ya yanke shawaran kunna wayoyin yana kunnawa ko kiran KHALEEL na shigowa,cike da nishad'i ya d'auka yana fad'in "MAN..! Yane..? ya iyali...?" "A'a ku ai kune masu iyali,tunda gashi ganin kama ya gagara bare a jika ko da a waya.." Murmushi yayi yana fad'in "Kai da Allah ba wannan ba,yanzun kana ina ne ina son mu had'u mu k'arasa maganar karatun JODI..." Dariya KHALEEL yayi yana fad'in "Ehh! lallaifa ka tabbata masoyi irin wannan canjin suna cikin lokaci kad'an haka.." Bai tanka masaba,saima hiran daya canja zuwa maganar daya d'auko na karatunta dayake so nan bada jimawa ba ace hakan ya samu. Sai da suka gama maganar sannan yayi masa sallama,d'agowa yayi yana kallon hanyan corridor na bed room ensu,tsaye ya ganta cikin gown data kamata red colour mai suphagetti'n hannu,gashinta ta kamashi a tsakiya da red en ribbon,idanunta ya sha kajol kwalli,da red en lipstick sai kyalli bakinta keyi..Kallonta ya tsaya yi kamar wani dolo,k'amshinta duk ya cika gurin,har tazo gabansa bai sani ba,sai data masa blowing air a fuska sannan ya sauke wani ajiyan zuciya,waist enta ya rik'e dai² tana shirin zama ya janyota kan laps nasa "Jodi wannan kwaliyyanfa haka..?" Hannunta d'aya ta zagaye a wuyansa d'ayan kuma tana zane akan fuskansa tana tafiya da shi daga kan goshinsa zuwa saman tip noise nasa,wani ajiyan zuciya yayi yana lumshe idanunsa kamar mai jin bacci,bud'ewa yayi ya sauke su kanta cikin shak'ak'k'iyar murya yake shirin yin magana sai dai kuma ya kasa,gyaran murya yayi yana son magana again ya kasa,yatsanta tasa a kan lips ensa tana shafawa kamar tana sa masa wani abu tana kallon cikin idonsa,sai data bari ya gama kamuwa dan idanunsa har sun soma sauya launi tayi saurin mik'ewa tayi hanyan bedroom a guje tana masa dariya.Binta yayi da sauri ko kafin ya k'araso ta turo k'ofan tana k'ok'arin rufewa,da sauri yasa jikinsa ya tareta,barin gurin tayi da gudu ta haura kan bed tana dariya,murmushi yayi ya kamota "Wato na zama abun tsokana a gurinki ko..?" Tana kallon eye ball nasa tana dariya,kallonta yayi yana matsawa da fuskansa,porehead nasu ya had'a sannan tip noise,har lokacin dariya take tana shirin yin magana ya hanata,dai² lokacin daya kamo lower lip nata yana kissing. Shiru tayi tana faman mutsu-mutsu,sai da yayi nisa sosai a jahar da bai san inda yake ba,ring en wayansa dake yashe kan bed ya dawo dashi hayyacinsa,a wahale ya d'ago jajayen idanunsa yana lalubarta da niyyan ya kashe ya d'auko,sai dai kuma sunan KHALEEL daya gani yasa shi d'auka,ko kafin yayi magana KHALEEL en ya katse shi ta hanyar fad'in "To mara zumunci gamu dai a parlour muna jiranku..." Wani uban tsaki ya saki,a fili ya furta "Banda d'an iska yanzun mu gama waya baka fad'aminba,sai yanzun saboda ka rainama mutane hankali.." Ransa a d'an b'ace ya koma gefe yayi rigingine yana murza goshinsa daya d'auki d'umi,dariyan mugunta tayi ta mik'e tana gyara riganta daya janye yayi sama,sai da taje bakin k'ofar fita ta juyo ta kalleshi,kallonta yake idanunsa sun canja kamar zai mata kuka yake kallonta,gwalo ta masa sannan ta fice,K'wafa yayi sannan ya furta "Zan kamaki ne,za kuma kiyi bayani.." Da kyar ya saita kansa ya fice,ko daya fito parlour nan ya shiga had'e fuska saboda bai son su kawo masa wasa,KHUBRA dake rik'e da hannun ZUHRA ta d'ago cikin alamu na rashin gaskiya ta kalleshi,aiko take suka had'a ido kallon da taga yayi mata yasa ta kwashewa da dariya,kallonsu KHALEEL da ZUHRA suka tsaya yi,sai dai kuma sun bagarar da lamarin babu wanda yayi magana,nan hira ya b'alle tsakaninsu,janye ZUHRA tayi suka shige d'akinta da suka gama chukuikuye bed sheet en kai kamar wad'anda sukayi dambe samansa,kallon yanayin d'akin ZUHRA tayi sannan ta kalli KHUBRA tana fad'in "CWEETY haka kika koma kuma...?" Cikin alamu na rashin fahimtan inda zancenta suka dosa ta kalleta tana fad'in "Me kuma akayi..?" "Can nake nufi..." Ta nuna mata saman bed enta,d'an tsaki tayi tana fad'in "Ke yanzu nefa ya koma haka,ai na gyara da safe..." Bata kuma magana ba,dan kam ba saita tambayaba,ta gane abunda take nufi,k'ulewa sukayi cikin d'akin tana koya mata wasu abubuwan a tunaninta KHUBRA bata san komai ba,ita ko kallonta kawai take,a zuciyarta fad'i take "Y'ar uwata kenan ke a ganinki dan na rayu a k'auye babu abunda na sani..Amma kuwa idan har haka ne to da zamana a nan bai amfana min komai ba,ko dan banyi boko ba ai hakan ba yana nufin babu abunda na iyaba,duk wannan soyayyar ai akwaita cikin ilimin addini,kuma akwai littafin da ABBANAH yake karantamin,hasalima sai dai na koya miki wani abun..." Tagumin da tayi ta zubawa ZUHRA ido,ita ZUHRA a tunaninta sauraronta take har ta k'are yi mata hud'ubar kwalliya dasa matsatstsun kaya wad'anda zasu jaa hankalinsa,tare suka shirya dinner su kuma su BB suna nan cikin parlour suna hiransu suma,har suka gama sannan KHUBRA ta wuce bed room inda tabar ZUHRA a gurinsu,wanka ta sake sannan ta shirya cikin short nicker iya cinyanta,da wani half vest,lafaya ta d'auko mai kauri ta nad'a sannan ta kama gashinta ta nad'e shi kamar yadda indiyawa suke yi yayi gammo,simple make-up tayi bakinta ya sha white lipgloss,sai k'yalli yake kamar an sanyashi cikin tandun mai,b'arin turare tayima jikinta sannan tayi juyi a gaban mirror,tana shirin fita ya shigo yana kiranta,tsaye yayi yana k'are mata kallo yadda ta koma masa kamar wata SONAM KAPOOR a cikin phrem rhatan dhan phayoo,hugging enta yayi ta baya suna tsaye gaban mirror en suna kallon juna ta ciki,a hankali ya juyo da ita suna fuskantar juna,hab'arta ya d'ago da hannunsa yana matso da fuskarsa dai² nata,cikin sauri ta dakatar da shi tana fad'in "YAYANAH kasanfa ba mu kad'aine cikin gidanba..." Idonsa ya runtse yana sakin wani gajeren tsaki,haushin su KHALEEL yake saboda zuwansu ya masa shamaki da kasancewa tare da ita,dariya take ta k'unshewa dan ta kula da yanayin da yake a ranar,kanta ta sunk'e tana yin k'asa da shi,hab'arta ya sake d'agowa yana fad'in "Bazan hanaki dariyaba,dan dama d'azunma har tsokanata kikeba kuma a gaban idonsu ko..?" Shiru tayi babu amsa sai idanunta da take juyawa tana kallonsa,wani killer smile ya saki yana fad'in "Tunda babu amsa nima baran barki ki fita haka nanaba,musamman wannan lips en naki da kika laftawa mai...emmmm! wai ma da haka zaki fita ne...?" Kallon rashin fahimta ta masa shi ko gira ya d'age mata,ita kuma ta kafe shi da ido tana jiran jin me zai fad'a,hannu yasa ya rufe mata ido a hankali ya had'e bakinsu guri guda,sai da ya tabbatar ya shanye lipgloss data sa tas,sannan yaja hannunta sukayi waje inda suka bar KHALEEL da ZUHRA na jiran fitowarsu,zaman da ZUHRA ke gyarawa ya tabbabtar da itama ba k'alau ba,d'an murmushi KHUBRA tayi tana d'auke kanta daga kansu ganin sai kame-kame ZUHRA'N keyi,haka dai suka gama dinner kafin sabon hira ya b'alle ZUHRA kam duk mamakin KHUBRA take yi,ganin yadda tayi shigan kamar indi'a a zuciyarta ko fad'i take "Lallai CWEETY ina miki kallon babu abunda kika iya a b'angaren soyayya ashe kyace sai dai ni na koya...Dole mana BB ya haukace miki,mai mata irin wannan ai dole ko wane lokaci a samu gadon baccinsu a yamutse.." Kallon agogo BB yake,dan tun d'azun shi yake ta kallo tun da akayi salla'n isha ganin babu maganar zasu tafi yasa ya fara magana fuska babu wani wadataccen fara'a "Wai ku kam sai yaushe zaku tafi ne...?" "Koranmu kuma za kayi ne..? ko kuwa dan mun zo gidan kane hakan..?" Banza yayi masa babu amsa,dan kansa kuma KHALEEL en ya kalli ZUHRA yana fad'in "HABEEBTEEY! Tashi mu tafi kinji tun yanzun an fara korarmu.." Kamar mai jira ko yana rufe baki ta mik'e tana had'a kayanta,suna gamawa KHALEEL ya kalli BB "To MAN! mu mun wuce tunda ka gaji da ganinmu.." "Ehh! ko me zaka fad'a sai dai ka fad'a bani kuma da lokacinka yau kam.." Murmushi KHALEEL yayi sannan ya kama hannun ZUHRA suka yi waje su kuma suna binsu a baya don rakasu.Sai da suka bar gidan sannan suka juyo da nufin komawa ciki,tafiyar da takeyi kamar bata so ne yaga ya masa tsayi janta yayi ta tsaya,kafin tayi magana ya rabata da k'asa,ko ba a fad'a mataba kam tasan nufinsa,hannayenta tasa ta zagaye wuyansa,kai tsaye bedroom ya wuce da ita yana sakin sanyayyar ajiyar zuciya dan kam tsawon kwana uku kenan ba tare da ya sake mata komai ba,yau kam ai sai yadda Allah yayi da ita dan ko ita da kanta ta tabbatar da haka,musamman yadda yake mata rawar k'afa tun safe,bare kuma yanzun da suke neman kad'aita da juna cikin d'aki d'aya shimfid'a kuma d'aya.................. *COMMENT FOR MORE PAGE'S........* 💃💃💃💃💃 *~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~* *_®єαl $mαѕhєr._* 😉 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/ SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVEL'S GROUP@web.facebook.com *©®2018* *5/ɑմցմՏԵ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~___________________________~* _Congratulations for the compilation of your amazing,wonderful and romantic novel dear *AMINA UMAR FANA (AUFANA)* Allah yasa sak'onki ya isarma al'ummar da akayi dominsu,Allah kuma ya baki ikon fara na gaba lafiya.._ *~___________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ 5⃣9⃣ *S* aman bed ya kwantar da ita sannan a hankali ya shiga warware lafayan data nad'a kamar sarii har ya kammala ware shi tas daga jikinta,arba yayi da arnan kayan dake mak'ale jikinta sam tunaninsa bai kawo masa cewa zata iya sa irin wad'annan kayanba,wani murmushi ne ya sake escaping daga bakinsa,sosai kayan dake jikinta suka amsheta musamman da suka kasance dai-dai ita,d'an nickers en nata ya kalla wanda da kad'an yafi pant da kuma mitsitsiyar rigar jikita wacce yanayin kwanciyan da tayi yasa halittun jikinta bayyana ta dai² wuyan rigan,da k'arfi ya sauke ajiyan zuciya saboda kasancewar irin rakin data yita ta zuba masa cikin satin aurensu yasa ya d'aga mata k'afa har na tsawon kwanaki uku,k'ark'arinsa da ita idan sun gama shirin kwanciya ta shige jikinsa kamar mage,shi kuma haka zai rungumeta ba tare da yayi mata komaiba,sai dai yau kam baya jin zai iya hak'uri musammanma yadda ta yita kunno shi tun safe,dole ne yau kam ya sauke mata gajiyan kwana uku.Tafiyan tsutsa ya soma mata daga cikinta har zuwa dai² chest enta da suka riga suketa tsokane masa ido,tafiyan tsuntsan da yake mata yasa ta shiga mirgina kai gefe tana dariya wanda yasa ta rufe idanunta,dariyan shima yake dan da alama kam tana enjoying abunda yake mata,ci gaba yayi ba tare daya sauraraba har hannayensa suka samu daman shigewa ta k'asan ficilar riganta wacce da kad'an tafi bra,salon da yake gabatar mata a lokacin shiya dad'a hautsinata lokaci guda service enta ya harba,romantic kisses ya shiga aika mata tun daga tafin k'afarta har ya haura zuwa saman maranta,daga nan yaci gaba da yin sama har ya iso dai² inda yayima hannayensa matsuguni yana wasa dasu,ruwan kisses en da yake sakar mata yasa itama batayi k'asa a guiwaba ta biye masa saboda kasancewar a cikin y'an kwanakin kusan za a iya cewa indai ta wannan fannin ne BB ya rigada ya gama biya mata babin,wanda itama babu b'ata lokaci ta haddace har tana neman k'ari,cike da shauk'i suke kissing juna wanda ya dad'a hautsina musu tunani kafin wani lokaci tuni har sunyi watsi da kayan dake sanye jikinsu,rumfa yayi mata suna kuma ci gaba da aikawa junansu sak'onni masu girma,wanda a k'arshen wannan dare sai da KHUBRA ta gane girman bambanci na halittarsu,dan kam BB ko kad'an bai saurara mataba sai da yaji network ensa ya kawo full,sannan ya koma gefe yana rungume da ita suna maida numfashi. Shi da kansa yakanyi mamakin dalilin da yasa ya koyi wannan jaraban bayan da ba haka yakeba musamman satinsu na farko da aure sam bai wani iya hak'uri,ko mene ne dalilin ohhoon masa,sai da suka gama maida numfashin wahala sannan yayi sama da ita sai toilet,cikin kumfan suka dad'a shantakewa ko tunanin dare yana ci gaba dayi basuyi ba,sai da suka shafe tsawon wani lokaci a ciki sannan daga bisani kuma sukayi abunda ya kaisu suka fito yana rungume da abarsa kamar baby'n robber.Bacci mai cike da shauk'i da kuma sukuni na kasancewarsu tare yayi gaba da su. *A MONTH LEAP.* A wata safiya bayan sun tashi kamar yadda suka saba suna manne da juna a haka suka had'a break fast,sun ciyar da junansu inda ya kasance fiye da rabin cin abincin nasu ya zama tsokana da haka dai suka kammala,sannan suka koma saman cuistion tana saman jikinsa cike da soyayya da kuma kulawa ya kalleta yana sakin mata k'ayataccen murmushinsa da ba kowa yake wa irinsaba,cikin k'asa da murya a dai² kunnenta ya furta "JODI yau kam ina so muje gida mu gaisa dasu MAMA fa..." Da sauri ta d'ago tana murmushi "Allah YAYANAH....? kamar kuwa kasan dama ina son ganinsu inata kewarsu fa.." Murmushi ya sake yi kafin ya d'aga mata kai cikin wani irin kallo mai wuyar fassara murya can k'asan mak'oshinsa ya furta "Mene ne abun kewarsu bayan kina tare dani...Ko kuwa kinfi sonsu fiye dani...?" Yatsanta ta d'ora kan lips ensa tana kad'a masa kai alamar a'a "Haba YAYANAH taya zaka ce haka,bayan kaine gaba d'aya rayuwata...Bana jin a duniya kam idan har a b'angaren soyayya ne idan aka cire son ALLAH da MANZONSA (S.A.W) daya zama wajibi akansu,sannan ABBANAH bana jin bayan wannan akwai wanda zai zo bayan nan sama da kai....Idan baka manta bama ai na fad'a maka da soyayyarka na girma tun ban gama sanin kainaba har ya zamana na fahimci hakan.Kaga ko idan haka ne wannan kalmar sai dai tayi gefe dan bata kamaci mutum irinka ba." Fuskarsa da matsanancin farin ciki yake kallonta kafin yayi magana yana kallon cikin eye ball enta "JODI ni kam ina son sanin ta yaya akayi kika gane ni a matsayin *MUTUMIN MAFARKINKI* dan wancan labarin kin b'oyemin baki sanar dani ba..." Murmushin itama tayi wanda ya bayyanar da hak'oranta cikin salon tsokana ta furta "Da wad'annan idanun naka masu kama dana kyanwa..." Sai da yayi dariya sosai sannan ya kalleta yana fad'in "A haka kuma kika gani kika mace a soyayyar mai idanun kyanwar ba..." "Eh! naji dad'in abunma dai ciwo bai kusa illatani ba.." Ta fad'a tana masa dariya,hancinta ya lakace yana ci gaba da dariya,sai daya tsagaita da dariyar sannan ya furta "JODI kin san wani abu..?" Kamar wanda zai fad'i wani abun kirki haka ta kalleshi tana fad'in "A'a YAYANAH sai ka fad'a zan sani..." "Idanki ai yana kama da nawa..." Dariya tasa masa tana fad'in "Haba dai ai nawa yafi naka kyau kallafa naka ta tsakiya wani haske dake ciki kamar na mage.." "Ok! tunda baki yarda ba zamu tambaya amma da *sharad'i* idan akace irin nawa ne zaki bani wani abu..." Ya k'arasa yana mata winking. "Hahhhh! YAYANAH sharad'i dai sharad'i dai ko wane lokaci kacemin kana da sharad'i,ni kuma na fad'a maka na daina yarda da sharad'in nan naka...Sai dai ka fad'i wani abun amma banda sharad'i..." Cikin shagwab'a ya furta "Ni gaskiya a'a shi kad'ai nake so,kuma idan baki yardaba zanyi miki kuka har sai kin rarrasheni da wannan abun zan hak'ura nayi shiru..." Yanayin da yayi magnar yasa ta kwashewa da dariya tana fad'in "Wai kam YAYANAH baka gajiya ne...?" "Dame zan gaji JODI.....? dake wai kike nufin zan gaji ko me..?" "Eh mana wancan satinfa sam baka barni na hutaba wannan ma haka...wai kam idan aka ce na haihu ya za kayi lokacin...?" Hak'oransa ne suka bayyana a fili yana mata murmushi cikin d'oki da farin ciki ya furta "Allah ameen JODI..ni yanzunma bank'i ace mun samu k'aruwa ba..yanzun ace cikin kwanakin nan nayi ajiyar baby a nan ai sai nafi kowa farin ciki.." Yana maganar yana shafa k'asan maranta,murmushi kad'ai tayi bata yi maganaba,hakan yasa shi fad'in "Ko bakya farin ciki ne JODI....?" "Me ka gani YAYANAH..." "Naji kinyi shiru ne daga maganar ciki,kuma bayan ke kika kawo zancen.." "Laaaa! YAYANAH me yasa bazan soba bayan ya fito ta sanadin abunda nafi k'auna,shirun da nayi wani abu nake tunani ne.." Da sauri ya dad'a rik'eta a jikinsa yana fad'in "Haba JODI bayan gani a gabanki wane tunani kuma za kiyi..?" "YAYANAH kenan ina tunanin ranar da za ace an kaini asibiti zan haihu ne...har na fara jin tsoro Allah.." _Dariya sosai maganarta ta bani nida nake gefe,cikin da ba ama tabbatar akwai ko babu ba shi ne har ake tunanin ranar haifeshi...Allah ya kyauta muku da kuke maganar cikinma._ "Laaaaa! JODI mene ne abun tsoro ai tare zamu haihu,kin san baran tab'a barinki kisha wahalaba duk rintsi muna tare a mak'ale da juna.." Mab'allan gaban rigarsa da suka kasance a bud'e wanda hakan ya bawa lallausan bak'in gashin dake kwance saman k'irjinsa damar bayyana,tasa hannu tana wasa dashi kanta kwance gefe tana ci gaba da abunda take,kamar wata k'aramar yarinya sai ta d'an ja a hankali ta saki tana sosa masa gurin wanda ya kasance kamar tafiyan tsutsa,a hankali ta kalleshi tana fad'in "Laaaaa! YAYANAH kacefa zamuje gida kaga kuma naga kana rufe ido Allah yasa ba bacci zaka ce za kayiba....ko kacemin na bari sai an jima..." Ido d'aya ya bud'e while the other one yana rufe "Sai zuwa anjima idan na gama abunda nake.." "To ammafa naga a kwance kawai kake,mai zai hana mu tafiya yanzun...?" Idanunsa a rufe duka ya furta "Na ce saina gama abunda nake.." "Ammafa YAYANAH...." Bakinta ya rufe yana fad'in "Bana son yawan maimaita magana mu barshi iya haka JODI,idan na tashi yanzun zan sake shiryawa.." "Shiri kuma wane iri..? canja kayan shi ne shiri kuma YAYANAH" "A'a ba iya changing kaya bane kad'ai.." Da mamaki a fuskarta take k'arewa fuskarsa kallo,coz maganarsa ta d'aure mata kai ta kuma kasa fahimtar abunda take nufi "Ni dai gaskiya YAYANAH ka tashi mu tafi kagafa idan rana yayi cewa za kayi sai wani lokacin...kuma ni Allah ina son zuwa kaji..." "Ok! muje kimin wanka to tunda kina so mu tafi yanzun..." Ba tare daya bud'e idanunsaba yayi maganar "Wankafa kace YAYA bayan tare mukayi wanka'n da kai...me zaisa ka sake wani sabon wankan kuma..?" "Kece.....! kece zaki sani sakewa.." Fuska da alamun tsoro tace "Nifa Allah YAYANAH banyi komaiba,ta ina na zama sanadin da zaka sake wanka kuma...?" Hannunta da take wasa da shi har lokacin a jikinsa ya rik'e yana fad'in "Saboda wannan abun da kike yi mana,ni kuma kinga baran ce ki bari ba..." "Hahhhh! YAYANAH haka ka koma kuma...Tabbb barin sauka a jikinka tun kafin wata ranama kace kwanciyan da nayi yasa ka....." Bakinta ta damk'e tana dariya jin irin rik'on da ya sake yi mata "Babu inda zaki je har sai kin k'arasa aikin kwangilar da kika amsa..." "Hahhhh! YAYANAH kenan ni dai nasan babu wani kwangila dana karb'a sai dai ko ban saniba yanzun za a bani..." "Uhmm! JODI kenan kwangila ai tuni kika karb'a signing ya rage kiyi..." "Gaskiya YAYANAH ban san yaushe ka koma haka ba..." 'Dagowa yayi yana kallonta idanunsa a kanta yake fad'in "Ke kika mai dani haka JODI tunda kinga ni lafiyayyen namiji ne,so dole sai kinyi hak'uri dani sannan kuma sai kin koyi juriya saboda mijinki..." "Yo to YAYANAH wane juriya kuma bayan wanda nake da ita har wani zan koya..." Dariya yayi mata "Noo! ina sone ki k'ara akan naki da kike da shi.." "Hahhhh! to ni dai gaskiya ka tashi mu shirya mu tafi...Kaji...?" "Ai sai kin k'arasa aikinki sannan zan yarda mu tafi,idan kuma bara kiyiba za a fasa tafiyan..." Ya fad'a teasingly yana kashe mata ido d'aya,fuskanta ta shagwab'e kamar za tayi kuka,da sauri ya dakatar da ita yana fad'in "Noo! kin san tun can bana son yawan kuka,so kuma abun nan it's a matter of deal,idan kin yarda shi kenan mu gama abunda ke gabanmu kafin mu tafi idan kuma ba haka ba shi kenan an fasa tafiyanma gaba d'aya.." Kallonsa take kamar sakarai saboda jin yadda yake ta tsara zance kai ta langab'e gefe bata iya cewa komaiba,ammafa idanun nan kamar wanda aka tsoma cikin ruwa "Yawwa! sannan idan kika yi kuka shima an fasa tafiyan yau sai wani lokacin..." Da sauri ta shiga maida hawayenta duk dan gudun kada a fasa tafiyan yau,bayan ta gama sawa a ranta zataje taga su MAMA... Wani killer smile ya saki yana dad'a janta jikinsa,idanunta a rufe saboda bata son tayi kuka coz tasan halin abunta tunda yace idan tayi za a fasa tsaf zai fasa en tun ba yauba tasan halinsa a d'an zaman da tayi a gidansu.Tana jinsa yana laluben bakinta ta bud'e masa dan kam a wannan lokacin gardama ba nata bane,sannan tun farko tayiwa kanta alk'awari duk abunda zai faru bazata tab'a hana shi hak'k'in saba duk runtsi,saboda a kullum abunda take tsoro kada ta hana shi Allah yayi fushi da ita,baya ga tsinuwar mala'iku da zata yita sauka akanta. _To k'alubalenku matan aure dama y'an mata masu niyyan yin aure,wasu suna d'aukan hakan a matsayin fansa idan miji ya musu laifi sai kuji ana cewa zamu had'u da shi a gado ne ai wallahi sai ya gane kuskurensa,shin y'ar uwa idan kika yi haka bakya tunanin faruwar wani abune kam? misali ya miki laifi yanzun shi kenan baki da wata hanya davzai gane ya miki laifi har sai kin had'a da bi ta wannan hanyar? to idan baki saniba ki bud'e kunnenki ko kad'an dan kinyi haka ba shi kika cutaba kanki kika cuta,kuma ki sani yin hakan tamkar kin d'auki wuk'ane kin dab'awa kanki,dan kuwa a lokacin da yake tsananin buk'atarki idan baki bashi kankiba to tabbas abunda ba a fata zai faru,imma dai ace daga wannan lokacin ya fara bin matan banza idan har da baya yi,imma kuma idan yana yi ya k'ara a kan na da,ya rage naki ki gyara ko karki gyara,amma kam tabbas idan kika yi haka k'arshe zaizo miki da sakamakon abunda kika jefaku ciki,sannan kuma ga tsinuwar mala'iku baya ga fushi da Allah zaiyi da ke,kafin kuma ki samu k'arin tsinuwar mutane ta soma yawo akanki,kinga saiki zab'a bashi hak'k'insa ko tsinuwar....Allah ya bamu ikon gyarawa._ Harshenta yake lalube ganin yana neman wahala ta mik'a masa nan yaci gaba da aikin dake gabansa,sai da suka gama jagwalgwala junansu sannan cike da farin ciki suka koma toilet,bayan sun gama shiryawa suka fito kai da ganinsu zaka gane wannan d'anyu ne a amarci,hannunsu sak'ale dana juna,ko a motanma yana driving hannunsa d'aya na cikin nata kamar wanda za a kwacewa ita,idan ya kalleta sai suma juna murmushi mai d'auke da sak'onni daban-daban haka har suka k'arasa mai house nasu. Ko gama daidaita parking bai yiba ta shiga k'ok'arin fita,da sauri ya dad'a rik'o hannunta,wani kallo wa watso mata idanunsa a narke yake kallonta,kanta ta sunkuyar k'asa da sauri "Saurin mene kike yi ne kam...Kina so mu koma ba tare da mun shigaba ko..?" Kanta ta shiga girgizawa kamar za tayi masa kuka,dariya yayi k'asa-k'asa "To idan kina so mu shiga ki bari mu tafi tare,bana son wannan gaggawa'n da kikeyi.." Dakatawa tayi har ya gama abunda yakeyi sannan ya fita,shi ya bud'e mata k'ofan ta fito cikin tafiyan sa ba zai ce tayi sauriba,hannunta ya rik'e a haka suka cimma parlour'n gidan. Sallamansu tasa MAMA da BABA ZUWAIRA fitowa daga kitchen suna fad'in "Maraba da amarya...." Hannunta ta fizge daga nasa tayi jikinsu da d'an gudu,rungumeta sukayi suna y'ar dariya game da tsokanarta tayi kyau kamar ba itaba. Bayan an gama gaisawa BB,ya mik'e yana fad'in "MAMA zanje wani guri na dawo,sai zuwa dare zamu koma in Allah ya kaimu..." Fatan alkhairi tayi masa,k'asa-k-asa yake kallon KHUBRA data wani mak'ale jikin MAMA ita kuma sai biye mata take ita ga mai y'a,har ya kai k'ofar palour yajiyo BABA ZUWAIRA nawa KHUBRA fad'an ta tashi taje suyi sallama,fuska ta kumbura kafin ta tashi ta biyo shi,har bakin mota ta rakashi yana gaba tana binsa a baya,kamar abun arziki ya bud'e motan ya shiga,ita kuma tana tsaye dafe da k'ofar ya d'ago ya kalleta ganin fuskarta a cukune yasa ya furta "Zo nan..." Babu musu ta zagaya ta d'ayan side en ta zauna tana kallon waje "Wato rakiyan ne bakya so shi ne kike wannan abun ko..? "Nifa ba haka bane..." "To yaya ne..?" "Babu komaifa..." Ta sake bashi amsa kuma har lokacin bata saki fuskar ba,juyo da ita yayi fuskarsu na kallon juna ta yanda suke iya jin numfashin junansu na sauka kan fuskokinsu "JODI nine baza ki iya rakowa ba sai an ce ki rakani...?" Kai ta girgiza idanunta a k'asa "Me yasa to kika b'ata fuskanki dan ance ki rakoni...? ko dan bakya so ne shi yasa..?" Nanma girgiza masa kai ta sakeyi "To mene ne..?" Shiru tayi shima shirun yayi ya jingina bayansa a jikin kujeran kallonta yaci gaba dayi,ba tare da ya mata maganaba,itama taci gaba da zama kanta a k'asa ta kasa magana. Sun jima zaune babu wanda yayiwa wani magana,shi kuma BB zuba mata ido yayi yaga iya gudun ruwanta,gajiya yayi da shirun ya fara magana fuska babu wani wadataccen fara'a "Wato baki san kinyi laifiba ko...?" Idanunta ne sukayi rau-rau za tayi kuka,kansa ya d'auke daga kallon da yake mata cikin muryar kuka ta furta "Kayi hak'uri YAYANAH dan Allah.." Dai² lokacin hawayen suka sakko kan fuskarta,kasa jurewa yayi da sauri ya furta "It's ok...!" Yana janta jikinsa yana patting bayanta,ajiyan zuciya ta sauke tana dad'a kwanciya jikinsa,sai daya tabbatar ya sanyata dariya sannan ya mata sallama akan sai anjiman idan ya dawo zasu tafi,cike da farin ciki ta juya suna waving wa junansu. Har dare tana gidan kowa sai nan-nan yake da ita musamman MAMA da FATAHIYYA,a nan su ABBA suka tarar da ita lokacin da suka dawo,sosai sunyi farin cikin ganinsu hankalinsu a kwance. A wannan lokacin ba kowa ne zai kalli ABBA'N KHUBRA ya shaida shiba,ashe dama wahala da zaman k'auye sukasa ya fara tsofewa,cikin y'an watanni har ya soma yin shar da shi,da yake Allah yayi shi mai tsafta shi yasa cikin lokaci kad'an ya dad'a gogewa musamman kuma daya had'u dasu ABBA mutanen da suka yi gogayya da turawa,yadda suke tafiyar da harkokin kasuwancinsu yanzun idan ba wanda ya san suba ba zai tab'a tunanin ba jini d'aya bane su en,dan mutane da dama suna musu kallon y'an uwan juna. Daf da zasu tafi KHUBRA ta matsa kusa da ABBA'NTA tana masa magana,cike da sha'awar ganin yadda y'ar tasa ta koma ya kalleta yana maida hankalinsa kanta dan ya fuskanci me zata fad'a,kamar abun arziki suka dad'a gaisawa yana tsokanarta,sai dariya take shi kuma hakan shi yasa shi yake sake jin dad'i sosai "ABBA dama fa akwai maganar da nake ta son maka.." Kallonta ya sake yi yana fad'in "To y'ar albarka ina sauraronki" Sai da tayi ajiyan zuciya sannan kuma kanta a k'asa tace "ABBA dama ba kan komai bane sai wani al'amari da nake ganin idan hakan ya kasance kowa zaiyi farin ciki..." Dad'a d'aure masa kai tayi saboda har lokacin bata fad'i abunda zata fad'a enba,muryarta ta katse shi daga sonyin magana "ABBA damafa shawara ne nazo da shi,nace me zai hana ka yarda da BABA ZUWAIRA a matsayin mata,kaga itama dama bata da aure mijinta ya jima da rasuwa,kuma ABBA na baku labarin yadda ta rik'eni na tabbata bata da wata matsala...Kuma kaima yanzun ABBA baka da kowa sai ni kad'ai..." Dakatar da ita yayi fuska a had'e yake fad'in "Maganar dama da kika zo da ita kenan saboda futsara irintaku ta y'ay'an zamani har ni kikewa maganar nayi aure...?" Yadda taga ya b'ata rai ya kuma zage yana ta mata fad'a yasa ta shiga bashi hak'uri,amma kam bata ji dad'iba daya k'i amincewa,haka sukayi sallama da mutanen gidan da suka rakosu har bakin mota kafin suyi musu sallama suka d'auki hanya. Cikin motan shiru babu mai magana kanta a k'asa tana matse hawayen dake sauka kan fuskarta,maganar BB ya dakatar da kukan nata "Me kika yiwa ABBA yayi miki fad'a....kin b'ata masa rai ko...?" Sai da ta gama kukanta ba tare data kula shiba,shi kuma sai nasiha yake mata yana nusar sa ita hanyar da zatabi su zauna lafiya da ABBA,sai da ta bari sunje gida har sunyi wanka sun kwanta sannan ta bashi labarin abunda ya had'asu,ajiyar zuciya yayi kafin ya nuna mata illar abunda tayi,sai yanzun ta fahimci laifinta dan kam tabbas ba ita ya kamata tayi masa maganar ba.Tun daga lokacin ta k'udurce a ranta duk hanyan da zata bi sai ta bi na ganin hak'anta ya cimma ruwa kuma zata dage da addu'ah akan Allah ya tabbatar da alkhairinsa................ _Wannan kenan.._ *COMMENT FOR MORE PAGE'S..........* 💃💃💃💃💃 *~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~* *_®єαl $mαѕhєr._* 😉 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/ SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVEL'S GROUP@web.facebook.com *©®2018* *6/ɑմցմՏԵ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~___________________________~* _cwєєt ѕíѕ *HALIMATUS-SADIYA MUHAMMAD (LEEMA)* ínα tαчαkí murnα dα fαrín cíkí nα gαmα wαnnαn nσvєl mαí cíkє dα d'umвín dαruѕѕα nα *IYA KU'DINKA* αllαh чα ѕα ѕαk'σnkí чα íѕα índα kíkє вuk'αtα αllαh чαѕα mutαnє ѕuчí αmfαní dα d'umвín вαѕírαrkí dα kíkα zuвє α cíkí dα ílímí dαkє cíkín lαвαrín..uвαngíjí чα k'αrα lαfíчα dα níѕαn kwαnα mαí αmfαní._ *#1 ♥ cwєєt lєєmαtєєч.* 😍 *~___________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ 6⃣0⃣ *K* imanin kwanaki biyu kenan da zuwansu gida,yauma yana zaune cikin parlour a lokacin KHUBRA na saman jikinsa kamar kowane lokaci da idan kaje zaka tarar dasu a hakan.Cike da so da kulawa ya kalleta yana fad'in "JODI yanzun idan aka ce kizo a kaiki makaranta shin kina so ko kuwa...?" Kallonsa tayi tana murmushi ba tare data ce komaiba,saima hannunta datake ci gaba da wasa da shi a jikinsa,ganin bata da niyyan magana yasa ya rik'e hannunta yana kuma kallon ta,a hankali ta d'aga kanta ta kalleshi tana murmushi "Shi ne kina ji ina miki magana bara ki amsaba...? kin san dai bana son haka ko...?" K'ure shi tayi da ido tana nazarin fuskarsa,ganin yanda yayi yasa ta d'an gyara kwanciyanta tana fad'in "Ni kam YAYANAH wani karatu ne zanyi yanzun...? ina ganin bani da wannan daman dan kam lokacina ya riga da ya wuce,wanda nake da shima na addini ya isarmin,amma kam nayi girma da zuwa makaranta yanzun.." Shiru yayi yana nazarin maganarta,lallaima yarinyar nan idan ba shirme irin nata ba,har wane girma ne za ace tayi yanzun da karatun,shi kam tabbas yana da burin ganinta tayi karatu,shirun da taji yayi babu magana yasa ta sake d'agowa tana fad'in "YAYANAH waima me ya kawo wannan maganar ne kam yanzun...?" Idanunsu sark'e cikin na juna yake fad'in "Wato kefa a ganinki nan kinyi girma da zuwa makaranta ko...?" Kai ta d'aga masa alamar eh,kuma har cikin zuciyarta take nufin hakan,d'an murmushi tayi kafin ta furta "To waima YAYANAH kawai sai na wani tafi na zauna haka nan gemai-gemai dani nace naje koyan karatu ko me..?" Da sauri ya katseta ta hanyar fad'in "Haba hajiya bafa wani girman da kikayi da karatu kuma da kike wannan maganar ma SHEHU JAHA ma cewa yayi acikin labarinsa *"GEMU BAYA HANA ILIMI"* sannan kinga kuma yanzun baki san wane irin y'ay'a Allah zai azurtamu da suba,shin bakya sha'awar ace kin bada naki gudunmawar ta b'angaren ginuwar iliminsu...?" Shiru ta sake yi tana nazarin maganarsa,ita kad'ai a zuciyarta take fad'in "Gaskiya dai kuma da haka,ko ba komai zanyi alfahari da kasancewar hakan idan har ya faru,to amma abun tambayan shin zan iya kuwa....?" Tambayan daya tsaya mata a rai kenan,ta kasa samun wani ya bata amsa,ganin jikinta yayi sanyi da maganar kuma da yiwuwar ya canja mata ra'ayi yasa baiyi k'asa a guiwa ba ya shiga kwad'aitar da ita amfanin karatun,wanda a k'arshe ya samu nasaran amincewarta,dan BB cewa yayi bazai mata doleba idan har ta nuna bata so zai bita a sannu har saita amince,saboda a nasa tunanin cewa yayi _"Duk abunda wani yake so wani yayi,idan har wanda ake so yayin ba shida sha'awar hakan to tabbas baza a samu nasara ba amma idan yana so nan ne zaka ga ya dage dan ganin ya aikata wannan abun kuma burinsa zaka tarar bai wuce na ganin yayi nasara ba"_ Murmushin samun nasara yayi yana shafa lallausan gashinta dake kwance yasha gyara "Uhmmm! JODI kenan wato kenan fa wai gani kike kin girma ko...?" "Haba mana YAYA kaimafa kasan na girma ai yanzun ai wani abun da zanyi shi da a yanzun kam ko da kud'i banyinsa,bare kuma da hankalina ai baranma soma aikatawa ba" "Gaskiya kam amma ni banga wani girman da kika yiba har yanzun" Mik'ewa tayi a jikinsa ta tsaya tana juya jikinta cikin salo tace "Haba YAYANAH kallenifa kaga yanda na koma hakama ai wani cewa zaiyi na zama uwar mata.." Dariya kalamanta suka sashi,sai dai kawai ya gintse yana kallonta yana murmushi,janyota yayi yana maidata muhallinta data tashi "Lallai kam babynah ta girma,amma wannan girman ai daban wanda nake nufi daban" "To wanne kake nufi kai...? ni dai nasan na girma yanzun" "Eh haka ne nima nasan kin k'ara girma amma ni barin fad'a miki irin wanda nake nufi.." Kallonsa taci gaba dayi tana sauraren jin me zai ce,hannunsa tajiyo k'asan cikinta yana shafa dai² mararta yake fad'in "Da ace kin girma ina tunanin ni ne mutum na farko da zai tabbatar da haka,kuma da nan gurin ya tabbatarmin da hakan koba haka bane..?" Sakin bakinta tayi tana kallonsa,lallaima YAYA'N nan nata ya rainata da yawa wato nufinsa har yanzun bata girmaba kenan yake nufi? Har sai ya ganta da ciki zai yarda lallai ne kuwa ta bashi mamaki kuma tabbas ta d'auki alk'awari saita nuna masa itan ta girma. Bata sake bi takan maganarba tayi cilli da ita gefe,idanunta ta lumshe tana jin yadda yake shafa k'asan cikinta ita kam bata san wane irine YAYA'N nata ba duk wani abu da zaiyi ya jefa zuciyar mutum cikin soyayya ya iya,gani take da ada ne aka tambayeta yaya halinsa yake zata ce babu ruwansa shi en kamili ne kuma bashi da fitina,amma kam a yanzun cikin d'an tak'aitaccen lokaci ta gama fuskantarsa a nata tunanin tsaf zata zane littafi hard cover da halayensa,katse mata tunani yayi da fad'in "JODI ki shi shiryafa cikin satin nan zaki fara zuwa makaranta" Daga haka bai k'ara ko wasalin 'a' ba ya d'inke bakinsa ta hanyar rufe idanunsa danma kada ta dameshi da tambayoyi,hakan data ga yayi yasa ta yin murmushi cikin sanyin murya ta furta "Allah ya kaimu,ubangiji kuma ya bamu sa'a..." Amsawa yayi yana yadda yake tare da sakin mata kiss a porehead enta,murmushi tayi tana sake tightening hands enta dake jikinsa,kamar masu bacci haka palour'n yayi shiru baka jin maganar kowa cikinsu amma kuma a hakan hira suke da junansu,kiran daya shigo wayan KHUBRA ne yasa ta d'ago ta kalleshi,shi enma ita yake kallo mik'ewa tayi daga jikinsa inda bayan ta d'auka kiran ta shiga gaida MAMA,tambayan da MAMA tayi mata ne yasa ta kallonsa da sauri kuma ta d'auke kanta tana ci gaba da sauraron maman dake maimaita mata tambayan "Doughter wai kam ina son tambayanki,ranan da kuka zo gida mai ya had'aki da ABBA ne kam har kika janyo ya miki fad'a...?" Ajiyar zuciya tayi kafin cikin sanyi ta shiga bawa MAMA labari bata b'oye mata komaiba,a b'angaren MAMA kam taji dad'i sosai da yarinyar tata tayi wannan tunanin sai dai kuma dalilin da yasa ABBA ya mata fad'a shine tayi k'aranta ta fad'a masa wannan maganar kamata yayi dama a samu mutum wanda yake babba mai cikakken hankali sai ya nusar da shi cikin hikima da siyasa,kuma tabbas al'amura zasu tafi yadda ya kamata idan haka ta faru. Nasiha tayi mata sosai akan ta kira shi ta bashi hak'uri sannan kuma kada ta sake yin maganar da kowa,haka dai har suka gama wayan ta ajiye,suka sake ci gaba da uzurin gabansu... Kwanaki sun ci gaba da wucewa yayin da kowace rana da zata zo ta wuce take tafe da nasarori masu d'umbin yawa.A bangaren su KHUBRA da BB ma hakan ce ta kasance inda maganar makarantar ta ya kankama,makaranta mai kyau wacce kuma zata koyi karatun babu wasa ya kaita,kuma alhamdulillah! al'amura na kyau sosai,shi da kansa yake kaita school sannan idan an tashi shi yake zuwa ya d'aukota,ko da ace yana office ranar da zaran lokacin komawanta gida yayi zai tattara abunda yake yi ya tafi,sai ya maidata gida sannan zai koma office ya k'arasa aikin ranar,wata ranar kuwa idan ya dawo tofa bai komawa sai dai gobe. Rayuwarta a makarantar wani lokacin idan ta kalli da yawan d'aliban sai taga akwai wanda ko a shekaru ya girme mata bare kuma girman jiki da wasu tsaf sai su d'auketa suyi ta gudu da ita ba tare da nuna gajiyaba,wani lokaci idan taga haka sai take tuna BB lokacin da yake mata maganar karatun,sai dai kaga tayi murmushi ita kad'ai. Zaune take k'ark'ashin wata bishiya tana duba littafinta da suka gama lesson,tayi nisa a dubawa taji an mata sallama,d'agowa tayi dan ita a tarihin zuwanta makarantar babu da wacce suke k'awance,wata y'ar matashiyar budurwa ta gani tsaye tana mata murmushi,kyakykyawa da ita son kowa k'in wanda ya nema bai samuba,cikin dakewa ta amsa mata suka gaisa a mutunce,kallonta waccan d'ayar tayi tana fad'in "Idan babu damuwa kuma ban takura mikiba shin zan iya zama...?" 'Dan murmushi KHUBRA tayi ganin itama da fara'a a fuskarta tayi maganar "Babu komai bismillah! ki zauna" "To ai kuwa na gode sosai da amsamin da kikayi.." Matashiyar ta fad'a kafin cikin d'an yanayi na kasancewarsu sababbi a gurin ta furta "Ni suna na AMINA UMAR FANA,nima sabuwar d'aliba ce a nan,to kuma ban san kowa ba a nan sai yau Allah yasa na ganki nayi kuma sha'awar miki magana ban sani ba ko zamu iya zama k'awaye.." "Allah sarki ai nima da yake sabuwar zuwa ce shi yasa kika ga na zauna nan saboda babu wanda na sani,amm! ni kuma suna na KHADIJAT ABUBAKAR SA'AD amma a gida ana kirana da KHUBRA.." Dukansu suka yi murmushi wa junansu,a hankali suka ci gaba da hira jefi-jefi kuma mafi yawanci duk akan karatunsu na ranar da suka yi ne,sosai tarayyarsu ta basu sha'awa ganin sun taimakawa juna da abunda d'aya ya gane d'aya bai ganeba,har lokacin tashinsu yayi,dai² lokacin aka zo d'aukan AMINA inda tayi ta yima KHUBRA magiyan tazo su tafi tare,hak'uri ta bata tana kuma fad'a mata itama yanzun za a zo d'aukanta,haka ta tafi wanda suna yin gaba BB yayi parking,glass en side ensa ya sauke yana kallonta,d'an murmushi tayi kafin ya fito ya bud'e mata ta shiga,sai da suka d'auki hanya ba tare da ya kalletaba yace "Wane mota na gani ya tsaya inda kike....?" Shiru ta masa babu amsa,shi kuma yaci gaba da fad'in "Kina sane da cewa ke matar aure ce ko...? to ina so ki kiyaye kule-kule babu ruwanki da kowa coz bana son fitina kinji me nace...kiyi abunda ya kawoki babu ruwanki da shiga abunda ba a sakiba kinji...?" Kanata ta d'aga alamar taji. Kwanaki biyu tsakani take bashi labarin AMINA da suka had'u a school irin kirkinta da kuma yadda suke zaune da juna,yaji dad'in yadda ta fad'a masa abunda ya had'asu kuma shima ya tabbatar da cewa yes matarsa kam y'ar baiwa ce,yanayin yadda yake zama suna lesson kan abunda aka musu a makaranta duk bayan sallar maghreb yasan tabbas baya asara... Tun bayan da sukayi magana da MAMA akan dalilin daya sa ya mata fad'a a wani zuwa da sukayi a can baya,MAMA bata b'oyewa ABBA'N su BB komaiba ta sanar masa cikin hikima da siyasa shi da ABBA'N KHALEEL suka sashi gaba da maganar,sosai suka kai ruwa rana da su wanda daga k'arshe kuma yaga rashin dacewar k'in amincewar da yayi tun farko,shi da kansa ya same su da maganar daga baya,cikin lokaci k'alilan aka gama magana,da taimakon MAMA da UMMI suka sata gaba itama kuma sai Allah ya taimaka basu wani sha wahala ba ta amince,an yanke d'aurin aure kad'ai za ayi sai tariya kuma babu wani taro da zasu yi bare mutane su fahimci wani abu game da sirrinsu,cikin lokaci kad'an aka d'aura auren ALHAJI ABUBAKAR SA'AD da amaryarsa HAJIYA ZUWAIRA akan sad'aki mafi inganci,anyi taro lafiya wanda y'ay'ane kad'ai suka halarta babu wata gayyata da suka yi daga iyayen sai su. ASHNA kam lokacin bikin tana ta fama da laulayin ciki kuma sosai take shan wahala,babban dalili kenan daya sa FATAHIYYA komawa gidanta tana taimaka mata,palour suka rashe sunata hira tsakaninsu BB,KHALEEL,SADEEQ BIGGY,KHUBRA,ZUHRA dama ASHNA dake fama da kanta amma a haka ta dage itafa saita zo dan baza ayi babu itaba,FATAHIYYA kam d'akinta na gidan ta tsere dan cewa tayi bata iya zama gaban yayyen nata da ko wanne yake manne da matarsa ita a nata ganin kam wannan fitsarar da suke gwadawa bata iyawa. Haka aka gama taro kowa ya d'auki matarsa yayi gaba,sai fatan samun zaman lafiya da sab'awar halaye. Lokaci baya jira sai dai a jira shi kamar yadda wannan magana take haka fa abubuwa suke,bayan kimanin watanni biyar da auren ABBA'N KHUBRA,ASHNA ta haifi zankad'ed'en saurayi Yaro yaci sunan ABBA'N BIGGY wato MUHAMMAD suna kiransa da AL-MUSTAPHA,fad'in hidimar suna da suka sha a wannan family'n b'ata baki ne,yayin da a b'angaren ZUHRA da KHUBRA kuma shiru kake ji babu wacce tayi ko da b'atan wata,sam hakan bai wani dame suba dan ganin samu da rashi duka daga Allah suke lokaci kad'an yake azurta mara shi kuma hakan ma ba abun damuwa bane tunda duka yaushe akayi auren da zasu d'aga hankalinsu,a b'angaren karatunta kuwa ta dad'a maida hankali sosai k'awancen su da AMINA kuwa sai abunda yayi gaba,mutane da dama suna mamakinsu wanda bayan tsayin watannin da suka shud'e kowacce ta san y'ar uwarta nada aure,k'awance na tsakani da Allah suke duk inda kaga d'aya cikin makaranta to zaka ga d'aya,mazajensu sun san juna yanzun baya ga ziyara da sukan kaiwa junansu,sun dad'a dagewa akan harkar karatunsu abunda ya kaisu shi suke yi babu wasa,tsakaninsu da mutane gaisuwa ce suna kuma matuk'ar girmama junansu. Yau tunda KHUBRA ta shigo skul take baza idanu taga inda aminiyar tata zata b'illo amma shiru kake ji,zaman makarantar duk ya isheta haka dai tayi manage har aka tashi,ko data koma gida bayan ta kirata a waya a kashe aka shaida mata,yinin ranar haka ta yini wani iri da ita wanda shi kansa BB sai da ya gane haka,ko da ya tambaya bata b'oye masa komaiba ta sanar masa,addu'ah ya nusar da ita tayi kan Allah yasa lafiya. Washe gari tana shiga skul ko ta hangota har ta rigata zuwa,da saurinta ta k'arasa kusa da ita tana fad'in "Haba CWEET SIS jiya kuma sai najiki shiru,kuma line wayanki a kashe haka naita fama da tunanin lafiya..." "Allah sarki y'ar uwa ta gari wallahi ki bari ke dai,ai ban baki labari ba,kwana biyu ne sai a slow wollah duk dare da wani irin zazzab'i nake kwana,shi nefa ogana yace lallai sai munje asibiti to ni nake k'in zuwa sai nace masa makaranta,shi nefa jiya na tashi da shi aiko shi ne yace mu tafi asibiti dana ce makaranta baki ga yadda yamin fad'aba har yana cewa lafiya ita ke gaba da komai.." "Kai amma naji dad'i daya miki haka banda abunki ai oga gaskiya ya fad'a..." "Ke dai bari kawai ai kuwa munje hankalinsa ya kwanta.." "To ya jikin hope komai normal...?" "Uhmm! ke dai bari inafa normal.." Da sauri KHUBRA ta kalleta tana fad'in "Kamar yaya kenan?" "Babu komaifa da wasa nake miki,da sauk'i sosai sai dai kun samu k'aruwa.." Wani ihu KHUBRA tayi tana rik'eta "Wayyoo! kice min ciwon kenan dama.....To Allah ya raba lafiya,ubangiji ya kawo mana su masu alkarka.." Wata y'ar class ensu ce ta lek'o da yake ta iya gulma da munafurci a makarantar coz idan kana neman expert ta munafukai ka samota to ka gama,nan take fad'in *"AUFANA* lafiya kuke ihu da wannan safiyar..?" Wani kallon k'asan ido KHUBRA ta mata tana fad'in "Lafiya k'alau ko kinji ance miki ba lau bane..?" "Au too..." Ta fad'a tana barin gurin,yadda AUFANA taga KHUBRA tayi da fuska yasa ta yin dariya tana fad'in "Kai CWEET SIS ki d'an saki fuska mana irin wannan had'e rai haka kamar wata BOSS.." Dariya dukansu sukayi AUFANA ta furta "Allah sarki harna tuna da wata mak'ociyata mai suna *JIDDAH* da take bani labarin yadda mijinta yake a da kafin a musu aure,wallahi ko da take fad'amin ita da sister enta *MEINERH LITTLE* sun sha wahalarsa shi yasa suke ce masa *YAH BOSS* amma kuma kafin aurensu da bayan sunyi aure data fuskanci halinsa shi kenan wai shi raini ne baya so shi yasa ya dinga musu haka.. Kuma yanzun haka wallahi idan kika ga yadda suke zuba luv sai kinyi mamaki,ammafa suna da kirki wollah musamman suka had'u su uku da wata sister en tasu mai suna *HUBBEEY* gaskiya ranar duk da suka zo har bana son mu rabu saboda y'an chapter ne.." "Allah sarki Allah ya bar musu zumuncinsu.." Inji KHUBRA dake k'ok'arin bud'e littafi don tana son yin nazari kafin malamin ya shigo "Ameen ya Allah...aiko wata rana Allah ya kawoki suna nan wallahi zaki ji dad'in kasancewa da su...yini d'aya idan kukayi da su wallahi ji za kiyi kamar kun shekara da su,Allah dai ya had'aku nasan zaki k'aru da zaman da za kiyi da su sosai.." Murmushi kawai KHUBRA tayi lokacin da take mai da hankalinta kan littafinta,itama AUFANA nan ta d'auko nata tana fad'in "Yawwa teacher KHUBRA yau kece malamata dan kinga jiya ban zoba saboda haka amin bayanin lesson en jiya,nasan dai kam YAYA'N ki bazai barki ba sai yayi miki karatu na musamman.." Dariya suka sake yi duka,can kuma suka tsunduma cikin karatu... Suna zaune suna karatunsu,wani malami ya taho zai wuce bayansa da wata d'aliba itanma dai baza ta wuce tsaransuba a shekaru kallon-kallo suka yi da ita,kafin suka ci gaba da abunda suke yi,har malamin ya gota su,sai kuma ya dawo yana tambayarsu wane class suke,fad'a masa suka yi ya juya ya kalli wannan d'alibar yana fad'in "Yawwa to kinga ga y'an uwa nan kin samu class enku d'aya da su,ki rik'esu su zasu baki masauki tunda sun jima a nan..." Godiya ta masa sannan ta musu sallama suka gaisa a mutunce ta nemi guri ta zauna kusa dasu tana sauraron yadda KHUBRA ke zubo bayani kamar wata lecturer.Saboda yadda take bayanin karatun ko malamin nasu yaji dole ne ya sara mata saboda wani abun ma bai bud'a musu bayaninsa kamar yadda take yiba yanzun,sai da suka gama sannan AUFANA ta kalli bak'uwar tasu tana fad'in "Sannu dai y'ar uwa..." A mutunce itama ta amsa mata tana murmushi,saboda itama ba dai arhar dariya ba.. AUFANA tace "Ni suna na AMINA UMAR FANA amma zaki iya kirana da AUFANA saboda sauk'ak'awa ma'anarsa kuma AU na farkon AUFANA yana nufin AMINA UMAR,shi ne idan kika had'a shi da FANA zai baki cikakken sunan,ita kuma y'ar uwata sunanta KHADIJA ABUBAKAR SA'AD,amma ana kiranta da KHUBRA." Murmushi ta sakeyi tana fad'in "Na gode sosai da amsata da kukayi...ni kuma sunana *MARYAM HAROUN SULAIMAN* amma ana kirana da *JANNAT*..." Hira suka d'an tab'a kafin suka koma class saboda ganin teacher na tahowa... Watanni sun sake zuwa har sun shud'e inda har sukayi jarabawoyi da dama wanda yanzun gashi har sun sake samun ci gaba na changing class.. Wata rana suna zaune suna hira su uku kasancewar yanzun sun zama su uku kuma k'awancensu babu algus cikinsa,suna ta hira a wata ziyara da suka kaiwa AUFANA da cikinta ya soma tsufa... AUFANA ce ta kalli KHUBRA da JANNAT tana fad'in "Sisters ena niko zanso jin labarinku da dalilin daya sa bakuyi karatu da wuriba musamman yadda naga Allah ya rufa muku asiri gidajenku da family enku babu talaka cikinku.." Kallonta sukayi duka suna murmushi saboda irin shak'uwar da sukayi da juna yasa suka san da wasu sirrika na junansu,KHUBRA ce tayi gyaran murya tana fad'in "Ai kuwa dai kam ya kamata musan dalilin dayasa mu duka haka ta faru damu,amma kafin naku bari kuji nawa...." Gyara zama sukayi dukansu,nan ta shiga basu labarin gwagwarmayar da tayi fama da shi a rayuwarta,sai dai kamar wancan lokacin data b'oyewa BABA ZUWAIRA farkon had'uwarsu haka suma ta b'oye musu da sa hannun MAMA a saceta,da kuma wasu abubuwa da suka faru a matsayinta na wacce bata son aga laifin iyaye da danginta..Bayan ta k'are su duka hawaye ne kwance a fuskokinsu suna jinjina labarin nata da tayiwa lak'abi da *Y'AR GARUWA..* "Lallai kin sha wahala sister amma haka Allah ya kaddara mana rayuwarmu...Badan lokaci daya k'ure ba dana baku nawa labarin sark'ak'iyata wanda nayiwa lak'abi da *"BAMBANCIN AL'ADU"* (My upcoming novel) amma ku biyo ni nan gaba in sha Allah duk ranar da muka sake samun sukuni zan baku labarina..." JANNAT ta fad'a,cike da alhini suka rabu ranar da tausayawa halin da KHUBRA ta shiga wanda har ya kaita ga fad'awa sana'ar *GARUWA*.............. *COMMENT FOR MORE PAGE'S.........* 💃💃💃💃💃 *~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~* *_®єαl $mαѕhєr._* 😉 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/ SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVEL'S GROUP@web.facebook.com *©®2018* *7/ɑմցմՏԵ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~___________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ 6⃣1⃣ *R* ayuwa nata dad'a tsayi zaman takewa na dad'a kawo shak'uwa da sabo baya ga k'imar juna da mutuntawa babu abunda ke yawo cikin wannan zuri'a ta *MALAM ABDU MAI ALMAJIRAI* wato *KAKA* duk wanda ya rab'esu ko to tabbas rabuwarsu bata zuwa face sun cika shi da d'umbin alkhairai. A b'angaren zaman aure zuwa mu'amala ko duka yaran nasu kawunansu a had'e yake,ko da surukin gidan wato SADEEQ BIGGY ba lallai ne mutum ya ganeshi a matsayin suruki ba sai dai d'a saboda yadda su ABBA suka d'aukeshi,hankali da nutsuwa ko a gurinsa duk wanda ya sanshi a baya idan ya kalleshi a yanzun ba zai iya shaida shi ba saboda nutsuwa da yayi,shi da kanshi wani lokacin idan ya zauna yana tuna rayuwarsa ta baya sai dai kaga yana zubda hawaye,yasan ba kowa ya sashi yin irin wannan rayuwar ba face kishiyar mahaifiya,ba dan yana da ilimin addini dana zamani ba da yanzun kam yasan rayuwarsa ta gama wulak'anta,dalili kenan da idan ya tuna sai yayi k'walla. Yaronsu ko AL'MUSTAPHA yanzun duk wanda ya kalle shi sai yayi mamakin girmansa saboda kulawa da ya samu cikin d'an lokaci yayi k'ato da shi. Soyayyar KHALEEL da ZUHRA a wannan lokaci kuwa kamar zasu had'iye juna musamman da idan suna hiran rayuwarsu na baya,baya ga kasancewar a bayan ba wani luv sukayi ba a matsayinsu na b'oyayyun masoya ga BB da KHUBRA,idan kaga suna exchanging words na soyayya to tabbata a waya ne ko suna chat da junansu,yanzun kuma da suka samu dama sai abun nasu ya k'etare sanin mai sani. Sosai KHUBRA ta maida hankali gurin karatu duk da dai kunsan rayuwar makaranta yau dad'i gobe akasin haka,amma a haka aka ci gaba da jalalla rayuwar da dad'i ko babu. Cikin shekara guda da rabi da aurensu ta dad'a girma na ban mamaki duk da a gurin shi gogan har yau idan hira ya kawo su kan maganar girma yakan fad'a mata bata girma ba,wannan maganafa ta BB tana hasala KHUBRA a duk lokacin da yayi ta,shiganta makaranta da had'uwa da sababbin k'awayen nata yasa ta k'ara wayewa da gogewa,ta wani b'angaren kam takan yiwa Allah godiya bisa ga ni'imomi da yayi mata. Yau tun da asubah da suka idar da sallah suka sake komawa cikin duvet,bacci mai dad'in gaske yayi gaba da su mak'ale da juna,sai wajen 10am sannan suka tashi cike da nishad'in zasu kasance tare a weekend en,su da kansu sun san zasu huta daga zurga-zurgan gurin aiki da skul.Sunyi wanka tare sannan suka had'a break fast kamar ko wane weekend suna cikin parlour zaune k'asa kan rug ya mik'e k'afafunsa,ita kuma tayi pillow da laps nasa,hiransu kamar kowane lokaci zuwa can maganar girma ya sake shigowa,cikin dariya da zolaya BB ya kalleta yana fad'in "Babu wani nan nifa har yanzun baki girma ba a gurina..." Kallonsa tayi k'asa-k'asa tana tab'e baki ba tare da ta kula shiba,shi kuma yaci gaba da tsokanarta "Bayan har yau komai ni nake miki ke ko gwadawa baki tab'a yi ai ko in dai haka ne babu ranar da zaki girma ko JODI na.....?" Kallonsa kawai ta sake yi tare da yin k'wafa yadda take rains mata hankali a ranta take fad'in "Yau kam zan baka mamaki YAYANAH....Amma barin ga iya naka gudun ruwan.." A hankali ta mik'e tana tafiya ta nufi hanyan bed room ensu,bata yi magana ba sai da taje dai² zata shige yace "Baby ina zaki je ne..Babu ko neman rakiya...?" "Ina dawowa YAYANAH yanzun abu zan d'auko na dawo..." Ta fad'a tana sake juyawa,bai bata amsa ba kawai dai ya d'aga mata kai alamar babu damuwa ita kuma ta shige.Yana nan zaune cikin parlour yaga ta d'an jima bata dawo ba,kamar zai bita kuma ya fasa tunawa da ta ce masa abu zata d'auko,ci gaba yayi da abunda yake a computer da yake akwai wasu detail's da yake son shigarwa,k'amshinta ne ya fara isowa cikin parlour'n bai d'agoba ya ci gaba da abunda yake yi har ta bayyana a cikin parlour'n,a hankali kuma ya kai kansa kanta ai ji yayi kamar numfashinsa zai d'auke saboda irin shigan da tayi kuma dama irin kayan duk ranar data sa tofa tabbas basa k'arewa ta dad'i,Nicker's ne jikinta bak'i dad'an rubutu na lemon a gefe ansa *STAR* sai d'an duwatsu dake gefen rubutun wanda aka k'awata shi da su,rigan jikinta kuma colour en lemon kasancewarta half kuma ba mai wani babban hannuba,yasa duk k'irjinta yake titi,sai bak'in takalmi na snickers data sa plat cover shoe,yadda ta tsara kayan a jikinta sun matuk'ar amsarta fiye da tunanin mai tunani,tana tsaye ta coge k'afa kamar mai shirin fita pick nick,gaba d'aya ta maida shi kamar wani idol ya daskare gurin,cikin takun ta na isa tana yi tana kad'a ilahirin jikinta har ta iso inda yake,k'afarta d'aya ta d'ora kan center table dake gabansa ya d'ora computer en cikin salonta tafurta "JAAN....ya kaga wannan kwaliyyan yayi kyau...?" "Sosaima kuwa yayi 100%...." Kanta ta d'an karkatar gefe sannan ta ce "Wait a minute....." Komawa ta sake yi cikin y'an mintuna ta sake dawowa da wani 3quarter jeas da body hug,shima da k'yar ya iya saita kansa ya amsa mata,haka ta sashi gaba ta shiga ta canja ta dawo,shi kuma yana fad'in tayi,last rigan ta d'auko wani transparerent riga multi colour,sai data gama dariyan mugunta tukun sannan ta b'alle bra en jikinta a haka tasa rigan shi kad'ai with out tasa pant ko bra,sakin gashinta tayi ya sauka har bayanta,sannan ta janyo wani hill en takalmi tasa,red lipstick ta shafa bakin tan nan kamar me saboda kyau duk da bata wani yi applying heavy make-up ba tayi kyau sosai,kaloj ta zizirawa idanunta,juyi tayi gaban mirror en duk jikinta babu abunda mutum bai hangowa,murmushi ta sakinma kanta kafin ta tasamma hanyan fita parlour gadan-gadan. Computer ya rufe idanunsa a kan hanya dan tuni ya bar aikin da yake yi,fitowanta yasa numfashinsa tafiya yajin aikin dole,coz baiyi tunanin ganinta a haka ba,babu abunda bai hangowa daga nan,tsayin rigan gaba d'ayansa kan cinyanta suka tsaya da k'yar ya had'iye yahun bakinsa idanunsa kam ko k'iftasu ya gagara yi,har ta iso gabansa,maimakon ta tsaya kamar sauran sai kawai jinta yayi saman cinyoyinsa hannunta d'aya ta zagaye wuyansa da shi,d'ayan kuma tana wasa da shi kan face masa kamar mai zana wani abu cikin muryan shagwab'a kamar za tayi kuka tace "JAA....AA....N.... anya nayi kyau kuwa...?" Bakinsa ya bud'e kalmomin na hard'ewa da kyar ya iya furta "Fi....fi....f...i....y....e....ye... da ko wane lokaci ma.." Y'ar dariya tayi mai sauti sannan ta shiga mutsu-mutsu kan laps nasa tana fad'in "Yawwa YAYANAH yanzun naji batu,kaga duk kayan dana sa wannan yafi kwantamin saboda amsan daka bani ya tabbatar min da haka barin je na cire to..." Tana shirin mik'ewa ya dawo da ita yana sakin mata wani kallo mai cike da sak'onni da dama,ko ba a fad'a mata ba ta fuskanci me yake nufi,amma ina sai ta nuna kamar bata gane ba ta marairaice masa tana fad'in "JAAN zan je nefa na cire kayan jikina kaga kada muyi bak'i su ganni haka..." Banda aikin had'iye yahu da kyar babu abunda yake cikin kunnenta ya furta "Noo! JODI muje zan cire miki da kaina..." Dariyanta ta k'unshe saboda yadda yayi maganar yana marairaice fuska kamar wani maraya sai langab'e kai yake cikin salon tsokana tace "A'a JAAN zan iya cirewa na dawo yanzun kaga na tabbatar wannan sunfi kyau duk cikin kayan..." Kallonta yayi da idanunsa da suka soma narkewa,ba tare da yayi magana ba yayi cupping fuskarta da hannayensa,yana kallon cikin idonta ya had'e bakinsu guri d'aya sun jima suna aikama da juna sak'onni da suka mance a inda suke,kafin yayi ciki da ita d'auke a hannunsa,tun kafin su k'arasa saman bed al'amura har sun dad'a tsanani,cike da nishad'i bayan samun nutsuwa suka sake sabon wanka,d'aure da towel iya cinyanta tana kan stool ta kalle shi tana murmushin mugunta tace "Wai kam YAYANAH d'azunfa kace wai kai baka yarda na girma ba ko...?" "Haba mana JODI sau nawa kike so na tabbatar miki da hakan,na fad'a miki babu abunda kika iya sai dai kullum ayi miki,duk ranar da kika yi k'ok'arin yimin abu d'aya kacal cikin abunda nake miki to ranar zan yarda kin girma kinga bama sai kin haihu ba kamar yadda mutane ke fad'a..." Ya k'arasa yana mata winking coz yasan ba abunda zata iya yi masa,y'ar dariya tayi tana kallonsa tace "Haka dai kace ko....?" "Yes! ai na jima ina fad'a kuma an kasa yi ba,so kawai ki yarda babu rana kwana kusa da zaki girma sai kin....." Bai k'arasa ba yaga ta k'araso gabansa ware towel en dake jikinta tayi had'e da wurga masa a kan fuska,a hankali ya d'auke shi yana dariya had'e da mata kallon lallai yarinya baki da wayo.Nasa ta bud'e had'e da shigewa ta rik'eshi ta baya coz bata so ya fad'i,passionately take kissing ensa kafin ta durk'usa a gabansa kan guiwoyinta ta cikin towel en,hannu tasa tana zare towel data bari jikinsa,kallonta yake yana dariya coz bai san me hakan ke nufi ba,zai yi magana ta hanashi saboda aikin data d'auko yafi k'arfin yayi magana,mamaki kam tun a nan ta gama bashi,yana nan tsaye ita kuma tana fama da service nasa,sai data gama lokacin BB babu bakin magana sai kallonta yake a duniya gani yake babu abunda za tayi ko cewa akayi za tayi zai k'aryata,yana kallo ta d'ago ta kalleshi ta saki mugun murmushi sannan ta kwanta jikinsa,a hankli taci gaba da haurawa har ta dawo dai² face nasa,wani sabon murmushi ta sake kafin ta sake had'e bakinsu tana zuba masa romantic kisses,yau kam gaba d'aya ta gama birki tashi in dai a wannan fagen ne,tsaf KHUBRA ta karb'e ragamar komai daga hannunsa,after komai ya lafa tana kwance samansa still,sai da suka gama maida numfashi suka koma toilet har lokacin kuma cike yake da mamakinta,ko da suka koma toilet again k'in bari tayi yayi wanka da kansa Lamar kowane lokaci,ko bayan da suka gama shirya juna suka dawo parlour tana kwance kan cinyansa har lokacin kuma ya kasa mata magana,ba tare da ta kalleshi ba ta furta "YAYANAH me yake damunka ne naji kayi shiru...." Fuskarsa dake d'auke da murmushin farin ciki ya kalleta yana shafa kanta cikin murya k'asa-k'asa ya furta "JODI yau kam kin gama bani mamaki har kinsa nama kasa magana..." Murmushin itama tayi tana fad'in "Dama ance ai 'Dan hakin daka raina wata rana shi zai tsokanema ido...." "Ai kam masu iya magana sunyi gaskiya dan nima yau gashi kin tsokanemin ido...wai dama JODI haka kike....? ni har ina rainaki kan babu abun da za ki iya." Dariya sosai tayi masa idanunta na fidda hawaye saboda yanayin yanda yayi maganar dole ne ayi dariya,ta mirgino tana kallonsa a ruf da ciki maranta taji yayi wani irin k'ullewa da sauri ta saki wani marayan ihu tana juyawa "Arrrrhhggg...! wayyo JAAN.." Rik'eta yayi da sauri ita kuma ta dafe mararta da sauri hannunsa ya d'ora kan nata yana fad'in "Me ya faru dake...?" Mararta take nuna masa sai runtse ido take shi kuma ya shiga mata massaging gurin yana mata sannu a hankali har taji gurin ya saki,bacci ne ya soma d'aukanta saboda dad'in abunda yake mata da taji zuwa can ta farka a d'an firgice tana mik'ewa,kamata yayi da sauri ya dawo da ita jikinsa "JAAN ka sake ni zanyi girkifa kaga na manta har na fara bacci kuma baka tasheniba..." "A'a JODI ina sane na k'i tashinki koma kiyi baccinki zan kula da komai.." Marairaicewa tayi tana fad'in "Please JAAN...ka barni nayi da kaina kagafa ba wani abu ke damuna ba,behind ma kuma na samu sauk'i bafa komai kawai ciwo ne lokaci d'aya kuma ya tafi naji sauk'i sosai.." Ganin ta dage yasa shi sakinta da sauri tayi hanyan kitchen shima ya bita a baya,tare suka fara shirya kayan da zasuyi amfani gurin girkin.Bayan kamar mintuna k'amshin girkin ya fara tasowa saboda tafasa daya fara yi,fuskarta ta fara yamutsawa kamar mai jin wani abu na daban,k'amshin ne yaci gaba da tasowa sosai ta yadda ba iya kitchen en ya tsaya ba har cikin parlour,da gudu ta fice a kichen en yanayin data fita yasa shi binta da sauri yana kiranta amma ina batama san yana yiba tun data shiga toilet en taketa faman kwara amai,jiyota yayi tana ta faman kakari a toilet da sauri ya shiga ya rik'eta yana faman jera mata sannu,sai da ta gama ya wanke mata bakinta ya sake rik'ota suka kamo hanyan dawowa parlour still k'amshin data sake shak'a yasa ta kwace jikinta da sauri ta juya tana sake yunk'urin amai sai dai wannan karon babu abunda ya fito daga cikinta face zallan kakarin da take,da k'yar ta dawo dai² d'aukanta yayi yana jera mata sannu saboda jiri dake neman kayar da ita tun a toilet,hanyan palour still ya kamo cikin wahalalliyan murya ta furta "YAYANAH kabarni nan banson jinwancan k'amshin..." 'Dan dakatawa yayi yana kallon yadda take magana,komawa yayi ya d'orata saman bed "JAAN sanyi nake ji please ka rufeni..." Tsigan jikinta duk ya tashi cike da tausayawa kamar zai mata kuka yayi saurin rufeta,sannan ya fice kitchen ya shiga yayi disconnecting duk wani abu na wuta dake ciki,komawa yayi gurinta ya tarar da ta shige ciki har kanta cikin tausayi yake kallonta shi kam bai tab'a ganin tayi irin wannan rashin lafiyan ba tun da suka yi aure idan aka d'auke ranar aurensu daya sameta kwance babu lafiya,da kyar ya iya samun nutsuwan kiran KHALEEL bayan ya masa bayanin komai cikin damuwa shi kuma ya nuna masa DR en family'n ya kamata ya kira,sai lokacin tunanin haka ya dawo masa yana kashewa ko ya kirashi,cikin mintuna k'alilan ya shaida masa zai iso. Lokacin da DR ya iso ya kira shi da kansa ya shiga dashi har inda take,babu b'ata lokaci yayi mata gwaje-gwajen da zai yi sannan ya tafi akan zai dawo nan bada jimawaba da sakamako... After some few hour's DR ya dawo da sakamako,jikin BB har rawa yake dan yaji meke damun JODI en nasa,cike da annashuwa a fuskar DR shi kuma daya kasa hak'uri har sauri yake ya tambaya sai dai DR ya katse shi da fad'in "Congratulations sir...." A ransa yake fad'in "Kaji bahago ina cikin tashin hankali kana min wani murna....toma akan wace uwar yake min murnan ne...?" Maganar DR ta dawo dashi hayyacinsa inda yake fad'in "Madam na d'auke da juna biyu na tsawon sati bakwai....Fatan Allah ya raba lafiya...sai dai kuma akwai abubuwa da za a kiyaye saboda ba wani k'wari yayi ba kuma idan ba a kiyaye ba to za a ita rasa abunda me cikintan,haka kuma yanayin abunda zata dinga ci dole ne ta dinga cin duk wani abu da zai gina musu jiki ita da baby'n...." Bayani sosai yayi masa sannan y zana masa prescriptions da za a nema yanzun wanda zasu taimaka mata..Bayan nan kuma ya masa sallama godiya BB yayi masa sosai,har bakin motansa ya rakashi sai da yaga tafiyansa sannan ya dawo da d'an gudu dan ya duba JODI en nasa,musamman yau da yake jinsa cikin k'ololuwar farin ciki wanda bazai iya misalta shiba................ *COMMENT FOR MORE PAGE'S..........* 💃💃💃💃💃💃 *~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~* *_®єαl $mαѕhєr._* 😉 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/ SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVEL'S GROUP@web.facebook.com *©®2018* *8/ɑմցմՏԵ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~___________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ 6⃣2⃣ *S* higa'nsa d'akin yana ta sauri dan ganin ya isketa,har lokacin tana a yadda ya barta,sai dai kam har lokacin idanunta a rufe suke ta takure guri d'aya saboda sanyin da take ji,yadda ya taddata sai ya tuno ranarta ta farko a gidan,kamar haka ya taddata ta k'udundune jikinta guri d'aya,still yayi yana k'are mata kallo,nan ya shiga tuno yadda sukayi a ranar,tunawansa babu b'ata lokaci ya raba jikinsa da kayan dake sanye a jikin nasa,a hankali ya haura saman bed en,ta cikin duvet en ya zare mata kayan jikinta had'e da rungumeta tsam cikin jikinsa,cikin kunnenta yake mata magana lokacin daya ga tana motsi yasan ta tashi ne. "JODI ina ke miki ciwo......? me kuma kike so...?" Yana magana yana shafa k'asan cikinta dai² maranta,sosai take enjoying abunda yake mata duk da kuwa ba wani k'arfi a jikintan,kanta ta girgiza masa alaman babu komai.. "Kin tabbata..?" Nanma nodding kanta tayi,ajiyar zuciya yayi yana fad'in "Oyyaahh! sanarmin mene za kici to kinji nasa a kawo miki..." Cikin wahalalliyar murya ta furta "Nifa na k'oshi..." "A'aa JODI kada muyi haka dake,na tabbata yanzun babu komai cikinki duk kin haras...look maza sanarmin..." "To ai dai na fad'a maka ban son komai,ni bacci zanyi kawai.." "Haba mana JODI kingafa cikinki yadda ya koma da ganin alamu kinsan kema babu komai,ko kuwa kina son barin baby'nmu da yunwa ne...?" Juyowa tayi da k'yar tana kallonsa a fili kuma ta maimaita kalmar "Baby'nmu kuma JAAN a ina kenan....?" 'Dan murmushinsa mai tsada yayi mata yana shafa mararta har lokacin ya furta "A nan mana JODI....don't u know u are pregnant....?" Wani murmushi ne ya sub'uce mata duk da irin halin da take ciki hakan bai hana murnarta bayyana ba,da sauri kuma ta maida fuskarta yadda take cikin magana irinta mai jinya ta kalleshi tana fad'in "Yama akayi ka sani bayan ni banga alaman haka ba...?" "Hahhhh! JODI kinji haushi ne dana fara sani....?" "Nop! YAYANAH kawai na kasa yarda ne ace ina da ciki yanzun.." Kallonta kawai yayi yana ci gaba da murmusawa abunsa shi kam ya tabbatar kuma da sannu itama zata tabbatar "Baby DR nefa ya sanarmin yanzun,ko baki san ya zoba ne...?" "Yanzu kuma..? yana ina DR...?" "Ya tafi..amma kam abunda ya fad'a kenan ga can sakamakon binciken daya kawo..." Ya mata showing inda resul en yake kan mirror,d'an kallon takardar kawai tayi,a ranta ko fata take Allah yasa haka ne dan ita babu abunda ta sani,hatta da zuwan DR en zuwa k'arin ruwan daya mata da allurai wanda BB ya cire mata time en daya k'are saboda haka ne yasa bata san da zuwan DR ba. Hannunta ta d'ora kan nasa suka ci gaba da aikin shafa gurin,idanunsa ya lumshe yana jin ranar yau a matsayin rana wacce tazo masa da al-khairai wanda ba zai tab'a mantawa ba,cikin kunnenta yaketa sauke mata sinka-sinka,container's,trailer's,basket kai da duk ma wani abu da idan kuka zuba bare d'aukeba dad'ad'an kalamai gameda sa mata albarka yake,ita kanta duk da halin da take ciki tana jin kalamansa har k'asan zuciyarta,jin kalamansa take kamar tafi kowace mace dace a duniyar da take rayuwa. Cikin awanni mafiya k'aranci har ta ji jikinta ya koma mata normal zazzab'in ya sauka,amma kuma har lokacin suna mak'ale da juna,kiran sallah ne ya tashe su daga hiran da suke,bayan yayi alwala ya fita masallaci,inda ya barta za tayi sallah nan cikin d'akin,bayan ta idar da salla'n tayi addu'o'inta,mik'ewa tayi ta d'auke pray mat en had'e da hijab en jikinta,bakin mirror en ta tsaya tana ware farar takardar da BB ya mata nuni d'azun,a hankali ta fara bin rubutun tana karantawa,farin ciki kam mara misaltuwa tayi shi,kan stool en ta hau hannunta rik'e da paper tana ta faman sakin smiling,hannunta ta mayar kan mararta tana feeling babynta dake kwance gurin,idanunta ta lumshe tana jan numfashi a hankali,k'arin hannu taji kan nata da sauri ta bud'e idonta duk da tasan ko waye wanda zai yi hakan,kallonsa tayi tana sake sakin murmushi,shima murmushin yayi mata sannan ya d'auketa suka fice a d'akin,suna tafe yana mata magana coz shi kam har yanzun bai hak'ura da maganar abinciba "JODI kink'i fad'in abunda zaki ci ko...? Kin san bana son zama da yunwa bare kuma ke...Kinga JODI maza sanarmin kinji...." Sai da tayi dariya sannan ta furta "Ni fa babu abunda zanci..." "A'a bana son jin wannan maganar daga bakinki idan kika ci gaba da fad'a zanyi fushi fa.." Ya fad'a yana b'ata fuska "A'a! a'a!! dan Allah kada kayi kaji YAYANAH cake kad'ai zanci da fruit juice..." Y'ar dariya yayi yana fad'in "Haba JODI wannan ai ba abinci bane kayan kwad'ayi ne..." "Ni Allah in ba shiba baran ci komaiba.." Cike da shagwab'a kamar za tayi kuka. "Ok! ok! an gama JODI..Kar kiyi kuka kinji..bari mu tafi mu siyo an fasa aiken kowa ma,kinga daga nan sai mu wuce gida ko...?" "Ehhh! kuwa dama ina son zuwa kawai ban fad'a maka bane..." Hancinta ya lakace yana fad'in "Ina fatan dai Babynah ba yawo zai sa mamansa ta koya ba..." "Haba YAYANAH kawai dan nace ina son zuwa...?" "Ehh! mana.....ammm! JODI kin san wani abu ma kuwa..?" Kallonsa tayi lokacin da yake sauketa cikin palour,da sauri ya koma ciki ba tare daya fad'i abunda yayi niyyaba,k'aton hijab ya d'auko mata har k'asa da plat en takalmi,da kansa yasa mata,ita kuma sai dariya take ganin yau wani sabon abu daya b'illo da shi,ita da bata fita da hijab sai in zata skul,yau kuma shi ne ya d'auko mata saboda neman magana irin tasa. "YAYANAH hijab fa ka samin.." Bata k'arasa ba ya katseta "Ehh! nafi sonsa yanzun gara ki saba saboda koda cikin ya fito bana son kina fita da vail wasu suna kallemin ke,kinsan a lokacin duk abunda zaki sa zaina showing jikinki sosai.." Y'ar dariya tayi kafin ya kama hannunta suka fice cike da nishad'i,bama kamar BB da yau jinsa yake kamar sabon ango. Sai da suka biya wani eatery suka siya cake da juice da take so,sannan suka d'auki hanyan gidan nasu suna tafe suna hira har suka k'arasa. HAJIYA ZUWAIRA zaune parlour dan kam yanzun ta jima da tashi daga matsayin da take da,shigowarsu KHUBRA ta haye kan jikinta tana kwanciya tana fad'in "UMMANAH nayi missing enki wollah kwana biyu kamar na shekara ban gankiba.." "Ke ni dad'ina dake kenan baki da aiki sai na son jiki kamar kyanwa,har yanzu baki san kin girma ba kekam.." BB dake gefe yayi dariya yana fad'in "A'a kam UMMA'NMU ai mun girma yanzun..." Kallonsa tayi tana fad'in "Inafa girma anan kana kallon babu abunda ya chanja a halin matarka na shegen son jiki..Nikam wannan ko haihuwa kikayi ina ga saikin koyawa y'ay'an son jiki dubafa ba dama taga mutum zaune yanzun ta d'afe mutum kamar ta samu katifa..." Dariya dukansu sukayi nan ta fiddo cake enta tana ci tana korawa da juice enta har taci da d'an dama,tana gamawa lokacin HAJIYA ZUWAIRA ta mik'e tayi kitchen,tashi KHUBRA tayi ta koma kusa da BB dake saman 3seater cuistion,ta kwanta kan cinyansa tana fad'in "YAYANAH yaushe zamu gidan CWEETY..?" 'Dan b'ata fuska yayi yana kallon cikin idonta "Wayyooo! YAYANAH mene ya faru naga ka canja fuska lokaci d'aya...Ko baka son kaini na ganta...?" Fuskarsa ya yamutsa kafin kamar wanda akayiwa dole yace "No...!" "To mene ne kasan nifa har ga Allah banso naga canji irin wannan a tare da kai,gani nake kamar na maka laifi mai girma..Please dan Allah ka fad'a min kaji.." Ta k'are maganar tata kamar za tayi kuka "Ehhemm! laifinma aikinyi kam.." Cikin d'an rikicewa ta mik'e daga jikinsa tana kallonsa lokacin har idonta ya gama cika taf da hawaye coz bata san laifin me tayi ba,ita kuma a rayuwarta abunda ta tsani ji kenan yace tayi masa laifi cikin rashin saninta,ranar ji za tayi rayuwarta ta mata k'unci "Dan Allah YAYANAH kaji ka sanar dani ko dan na gyara..Please kaji HAYATEEY...!" Banda dariya babu abunda BB yake k'unshewa saboda yadda tayi daf hawayenta suke da zubowa,shi kuma sai wainata yake,tunawa yayi da maganar DR inda yake shaida masa ba'a son mace mai ciki ta dinga shiga damuwa ko sa abu a ranta,hakan zai janyo mata matsala.. Da sauri ya saki fuskarsa yana kamota,kwantar da kanta yayi saman sholder ensa ta dama cikin rarrashi yake fad'in "Sorry JODI ba wani abu mai tsanani bane da zaki tada hankalinki kinji ko...Kwantar da hankalinki kinji.." "Ni dai ka fad'amin dan Allah..." Dai² lokacin hawayen dake idonta suka sakko,d'uminsu ya jiyo saman sholder ensa da sauri ya d'agota yana zare ido "JODI mene haka kuma..kin sanfa bana son haka ko..shi ne amma kike yi..." Ya fad'a yana dad'a maida fuskarsa alamun da tasan babu wasa cikin maganar da tayi,kece masa tayi da kuka cikin kukan take fad'in "To ba kaine kace na maka laifiba kuma na tambaya kak'i fad'amin...." Kansa ya dafe yana fad'in "Ya salaam...!" _Ni da nake gefe nace "Kujimin d'an malfar uba bayan shi ya janyo take kukan kuma yake d'aure fuska,kai wannan koi mai murd'ad'd'en hali..ka ce an maka laifi kuma kak'i fad'a...bahago kawai.."_ 😣 Fuskarta ya rik'e da hannayensa,bakinsa ya kai dai² inda hawayen ke bi,nan ya shiga d'auke mata su,dalili kenan daya sa kukanta tsayawa tana kallonsa,murmushi ya mata bayan ya gama d'auke mata hawayen,idonta na dama ya sumbata sannan na hagu,bakinta ya nufo da sauri ta kulle bakinta tana raba ido.Kallon yadda tayi yasa shi b'ata fuska,kamar za tayi kuka ta furta "YAYANAH bafa gida muke ba.." Sai lokacin ya juya ya kalli inda suke,kunya ce ta kama shi ganin ya kusa aikata ba dai²ba a gidan surukai,amma ganin babu kowa yasa shi bata fake kan bakinta,wanda bata yi tsammanin samunsa a lokacin ba. "Ni ka fad'amin abunda kake b'oyewa.." Ta fad'a tana turo d'an bakinta gaba,bakin ya kalla yana murmushin mugunta "Ok! amma ki daina min wannan turo bakin kinsan duk lokacin da kikayi ina kasa controlling kaina..." Murmushine ya sub'uce mata nan ya sata gaba yana tsokana *"MAI KUKA TANA DARIYA....AI MATA 'DAN KWA'DON DADDAWA...!* *MAI KUKA TANA DARIYA....AI MATA 'DAN KWA'DON DADDAWA...!!"* Dariya ta fashe da shi sosai,shi kuma nan ya shagala da kallonta yana kuma ci gaba da tsokanarta kamar wani k'aramin yaro.. UMMA'NSU ce ta fito da plate a hannu,zama tayi tana fad'in idan kin gama shagwab'ar to ga abinci can na jiranku a teburi. Kallon plate en data ajiye gabanta tayi nan ko ta hango d'an wake da manja,ai tuni yahunta ya fara gudu,cikin sauri ta sauka kan jikinsa,gaban plate en ta isa tana zuwa kuwa ta sure shi babu ko magana ta zauna nan k'asa ta soma cin abunta har dasu lumshe ido,kallonta kawai sukeyi shi kam BB dad'i yaji sosai daya ga tana cin abincin,ita ko UMMA ZUWAIRA sakin bakinta tayi tana kallon ikon Allah,can kuma ta saki murmushi saboda wani tunani da tayi,a fili ta furta "To to to..! ince ko dai mun samu k'aruwane take wannan zalamar...abunda nasan ba halinta bane..?" Daroya BB yayi yana d'aga mata kai dan shi ta kalla tayi maganar,wani murmushin ta sake yi tana fad'in "To! ko da naji...Allah ya inganta,Allah kuma ya raba lafiya.." Fuskarta da matsanancin farin ciki na jin zasu samu jika kwana kusa,kallonsu suka maida kanta suna ta hira tsakaninsu,amma ina sam KHUBRA bata sanma abunda suke yiba har ta kammala sannan ta shiga tsotse yatsunta d'aya bayan d'aya,kallonta sukayi suna murmushi "Haba KHUBRA zafa ki cire hannunki kan tsotsan da kike musu.." 'Dagowa tayi ta kallesu had'e da yin murmushi,sob'on data gani cikin cup ta d'auka ta tultulawa tumbinta,kan tsaban dad'in da yayi mata har lumshe ido take,da kyar ta mik'e tayi hanyan kitchen hannunta d'auke da plate data yashe abincin ciki,ko data fito BB ta nufa tana zuwa ko tayi pillow da cinyansa,take ko bacci mai d'ankaren dad'i ya kwasheta. Sai after asr ta farka ta ganta kwance kan pillow na cuistion en,d'an waigawa tayi tana kallon cikin parlour'n,dai² lokacin ya shigo a hankali ta sauke k'afafunta k'asa ta mik'e tana tafiya inda yake,warm hug ta bashi tana dad'a lumshe idanu "Baccin ne bai ishekiba ne...?" Kanta ta d'aga masa,ok muje to kiyi sallah saimu tafi gida.." Hannunta ya kama sukayi ciki,inda ya taimaka mata tayi alwala,a gabansa tayi salla'nta tana addu'ah shima ya d'aga nasa hannun,da yake su kad'ai ne cikin d'akin bayan ta k'are ya zare mata hijab en yana fad'in "Kawo nan muje ki huta saimu tafi anjima ko..?" Kai ta d'aga masa tana yin gaba a parlour suka dad'a rashewa ita kuma UMMA ta lek'o jin kamar magana "A'a ashe ka dawo..." "Ehh amma ban jimaba ma da shigowa ba." "Ayyahh! sannu da dawowa.." Amsawa yayi,ita kuma ta maida kallonta kan KHUBRA tana fad'in "KHUBRATU zaki ci wani abu ne yanzun....?" "A'a na k'oshi sai dai ko anjima.." "To shi kenan.." Kitchen ta koma taci gaba da aikin gabanta,kallonsa tayi nan ta tuna da abincin da aka ce suci d'azun,ita kam tun bayan data ci nata bata saniba ko shi en yaci,saurin kallonsa tayi tana fad'in "JAAN kaci abincin kuwa...?" Kai ya kad'a mata alamar a'a,da fuskarsa da ya maidata kamar wani yaro,da sauri ta sauke k'afafunta k'asa har tana neman fad'owa,saurin rik'eta yayi yana fad'in "Easy JODI.....Ina zuwa kike sauri haka,bakya tsoron ki fad'i ne kam..ko kuwa kin manta yanzun bake d'aya bace...?" Marairaicewa tayi kamar za tayi kuka "Abinci fa zan kawo maka..." Bakinta ya rufe da hannunsa yana d'an murmushi "No kada ki damu naci abinci d'azun,UMMA ta bani kina bacci..." Sai lokacin tayi sanyayyar ajiyar zuciya,sannan ta koma ta kwanta,can ta fara magana "JAAN inafa binka bashi.." "Uhhummm! ina jinki na mene bashin...?" "Maganar d'azu..." Ta bashi amsa a tak'aice "Ohhh! ni kingama har na manta,amma ke da yake kin damu da ji kin kasa mantawa.." Batayi maganaba sai wasa da take da yatsun hannunsa dake cikin nata,dai² kunnenta ya kai bakinsa yana fad'in "Kin san laifin da kika min..?" Har cikin ranta ta girgiza masa kai "Kina kirana da suna biyu,so na kasa bambancewa wanne nawa wanne ne kuma ba nawa ba." Kallonsa tayi shi kuma ya mata winking "Duka mana...ai duk naka ne.." Cike da shagwab'a yake fad'in "Ni dai a'a gaskiya sai dai a zab'i d'aya...Kuma bana son wannan YAYA'N da ake fad'a.." Y'ar dariya tayi tana fad'in "As u wish yallab'ai..." Ido ya fiddo yana fad'in "Kinga ni ba yanzun ma kin sake k'aramin wani...ko..?" Tana murmushi take fad'in "To MY JAAN an daina daga yau..." Dariya sukayi ta sake maida kanta ta kwantar tana hamma.." A tak'aice dai basu suka tafiba sai wajejen 9pm shima ABBA ne ya korasu. Suna tafe a mota ta zame ta kwantar da kanta kan cinyarsa,while shi kuma yana driving,bacci ne ya d'aukenta cikin alamu na magagin bacci can hannunta ta motsa duk a cikin bacci aiko nan ya tafi wata jiha ta daban,da sauri BB ya take burki,Allah ma yaso su titin babu yawan cinkoson abun hawa,gefe ya gangara sannan ya d'an dubata,gani yayi batama san abunda yake faruwa ba,d'an murmushi yayi ya gyara mata kwanciyar,sannan ya mik'i hanyan da zata maida su gida,har bedroom ya kaita,sai bayan ya ajiyeta ta bud'e ido "Ina zaka tafi JAAN...?" 'Dan waiwayowa yayi ya kalleta "No JODI zanyi wankane na dawo..." "Shi ne kuma ni bara ka yiminba...?" "Sorry naga kina bacci ni kuma kin san bana son abunda zai tada ki a baccin.." "To ai na tashi yanzun,kasan baran iya bacci haka nan ba.." "To tsaya na cire miki kayan ko..?" Kai ta d'aga masa alamar toh,a hankali ya tako ya dawo gabanta,sannan ya cire mata,towel ya d'aura mata sannan ya d'auketa sukayi toilet. Sun d'an jima ciki kafin suka fito,yadda suka fito yasa nace 'Ikon Allah wai nasara da gwado' kunsan me na gani....? Towel ne guda d'aya sanye jikinsu KHUBRA ta rik'esa ta gaba,k'afafunta akan nasa,hannayensa zagaye da ita ta gaba,yana tafiya dasu a haka sunata faman shek'a dariya.Shi ya fara zama saman stool en sannan ita dake kan cinyansa suna kallon mirror "Sauka na miki shafa ko..?" "Tabbb! wollahi baran sauka ba,salon haka kawai kasa y'an group en *SMASHER & HUBBEEY 1&2,SHDG NOVELLA,SHDG COMMENT'S ONLY,LEEMA FAN'S GROUP,SAWWAMA FA'NS GROUP,BARKIN'DO & MUHIBBAT* 😜su k'aremin kallo,Allah babu inda zani,naga dai kaika cillamin nawa cikin ruwa,sannan kuma kace na sauka Allah saika samin kayana zan sauka.." Dariya yayi mata yana mata gwalo ta cikin madubin "Yarinya ai sun riga da sun ganki tun a toilet lokacin ina miki wanka..." Kukan shagwab'a tasa masa tana bugun k'irjinsa "Allah ni babu wanda ya ganni.." "Sorry haka ne babu wanda ya ganki yi shiru to kada kiyi kuka..." Bakinta ta murgud'a masa ta cikin mirror,tana kallonsa ya d'an cije lower lip nasa,kansa ya d'an sauke k'asa dai² kunnenta ya furta "Idan ba tsoroba idan mun kwanta ki sake min haka ki gani..." Kallonsa tayi ta masa fari da ido had'e da sake murgud'a masa bakin "Yanzuma na sake me zaka iya yi...?" "Haahh! yarinya ai tsoro kike ji shi yasa kikayi a nan,amma ki bari mu gama kinji..." Murmushin mugunta ya mata ta cikin madubin,da k'yar suka gama abunda suke sannan ya d'auko musu nighty ensu,wani guntun singlet yasa mata mai d'an fad'i tsayinta duka bai kai kan knee's entaba,sannan ya d'auketa zuwa saman bed,ko daya direta fita yayi ya kashe duk kayan wutan dake gidan had'e da kullewa,bayan nan ya dawo ya kashe light en d'akin,kusa da ita ya kwanta ita kuma tayi saurin matsowa jikinsa.. "Wa na kama...?" Ya fad'a lokacin data gama shigewa jikinsa yana mata cakul-kuli,dariya ta shiga kyal-kyalawa tana fad'in "N....ii...Ka....kama..!" "Ohh! na zata zaki ce ba keba ai....oyaaa! muyi bacci to kinji..?" Kanta ta kad'a tana goge hawayen daya ziraro mata gefen idonta.Fake ya sakar mata a porehead daga haka bacci mai cike da nutsuwa ya d'auketa.............. *Aradu kwana biyu kunamin abunda ranku ke so,to nima zan muku abunda nake so,BB ya auri KHUBRA wato comment's kuma kun daina ko.....? Masuyi kad'an ne,so zan rage posting kullum nd yawan typing enma haka,zan maidasa 1 READ MORE kamar na cweet hulbateey...* *~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~* *_®єαl $mαѕhєr._* 😉 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/ SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVEL'S GROUP@web.facebook.com *©®2018* *9/ɑմցմՏԵ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~___________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ 6⃣3⃣ *H* ar tayi bacci shi kam idonsa a bud'e yake ya rasa me yasa ya kasa bacci a daren,farin cikinsa sam ya kasa b'oyuwa,yanda al'amuran suka faru yake ta tunawa,bayan d'umbin farin cikin data sa shi a safiyar,ta sake bashi wani bayan d'an tak'aitaccen lokaci wanda yafi kowanne zame masa abun farin ciki,shi ne yadda a ranar ta bayyanar masa a matsayin tana d'auke da juna biyu na y'ay'ansa,shi kam a yau bai san me zai mata wanda zai biyata d'umbin farin cikin data sashi ba,a ganinsa komai yayi mata bai biyata ba kan farin cikin data haifar masa,dad'a rungumeta yayi a jikinsa yana jin kamar ya maidata jikinsa su koma abu d'aya,sai da ya bari baccinta yayi nisa sosai sannan ya mik'e cikin yanayin da ya san bazai tashe ta ba,pillow yasa mata a inda ya tashi sannan ya rufe mata jikinta,fake ya sakar mata a porehead sannan ya shige toilet yana murmushi. Wudu'u ya d'aura sannan ya fito had'e da saka jallabiyya ya shimfid'a pray mat ya hau kai had'e da kabbara,sallah ya shiga jerowa duk sujuda sai ya jima cikinta yana musu addu'a ta neman zaman lafiya,kariya da kwanciyar hankali,tare da neman zuri'a d'ayyiba. Kusan k'arfe 2am sannan ya idar yayi addu'o'i a sauk'ak'e saboda yadda ya fara jin bacci,a nan ya bar pray mat en ya haura kusa da ita yana dad'a mannata da jikinsa,cikin lokaci k'alilan bacci mai nauyi game da dad'i ya d'aukeshi... Haka rayuwarsu ta cigaba da tafiya a yayinda ko wace rana take zuwa musu yadda suke fata da burin takasance,cike da soyayyar junansu suke kasancewa a ko wane weekends coz sauran ranaku ba wani isashshen lokaci gare su ba,amma idan aka ce weekend ya zo to nan zaka iske su tare komai kuma nasu tare suke aiwatar da shi,yadda suke gudanar da soyayyarsu da rayuwarsu a sauk'ak'e babu wanda zai gansu yaji basu birge shiba hasalima sai kaga mutum na kwad'ayin kwaikwayonsu... Cikinta ya dad'a girma inda yanzun yake da wata takwas da y'an kwanaki,zuwa yanzun ya zamana babu inda take zuwa tana zaune gida,shikansa BB wannan dalilin yasa shi d'aukan hutu gurin aikin nasu duk kuwa da dama company ne nasu ABBA suke aiki dukansu ciki,so wannan yasa bai wani samu matsala da hakan ba inda ya damk'a ragamar hannun KHALEEL,sai dai wani lokaci yakan lek'a ya ga yadda al'amura ke wakana. Suna zaune cikin parlour a k'asa kan rug,daga ita sai singlet mai d'an fad'i na shan iska kasancewar yadda cikin ya maidata gaba d'aya ta k'ara bud'ewa,k'afafunta a mik'e duk sun kumbura sosai babu mai kallonta yace cikin watansa takwas saboda mugun girman da yayi,shi kuma MR KHALEED sai aikin matsa mata su yake,jingina bayanta tayi jikin cuistion hannunta dafe da plate na fruit da aka yanka tana ci da fork,wani ta soko jikin fork en tana dariya tayi saitin bakinsa da shi,sai data bari ya bud'e bakinsa saita janye hannunta ta nufi bakinta da abunta tana masa dariya,kai ya kad'a mata alamar zai rama yana maida face nasa alamun yayi fushi. "Sorry JAAN....!" Ta fad'a tana kallonsa,d'auke kansa yayi yana ci gaba da b'ata fuska,wani ta d'auko tana sake kawowa dai² bakinsa,kamar bazai bud'e ba kuma sai ya bud'e,sake janyewa tayi tana masa dariya. "Kingafa kina d'aukan hak'k'ina JODI idan ba bani za kiyiba kibar abinki nima idan na tashi babu abunda zaisa na sammiki nawa.." "Haba mana JAAN kasan fa ni taka ce,kuma dai nasan zaka sammin ko...?" Tayi maganar cike da shagwab'a tana kashe masa ido d'aya "Haba yarinya babu wani wayo da zakimin kijima na fad'a miki.." "Haba mana...nicefa...." Still fuskarsa tana yadda take,yana kuma ci gaba da matsa mata k'afafuntan,janye k'afar tayi ta matsa kusa dashi kallonta kawai ya tsaya yi ganin ta janye k'afan nata kuma ta matso kusa da shi,kan cinyansa ta hau tana zagaye wuyansa da hannunta d'aya,while d'ayan kuma still da fork a cikinsa,grapes ta chaka ta kaishi bakinta,sai data gama melting ensa sannan ta kalli cikin eyeballs ensa tana kuma nufan bakinsa da nata,tun kafin ta k'arasa ya fahimci nufinta,wani murmushi ya sake mata yana dad'a rik'eta sosai a jikinsa,nasa ya bud'e ita kuma ta shiga zuba masa ruwan narkakken grapes en,licking mouth nata ya shiga yi,daga haka wasa ya canja salo,nan suka lula cikin wata duniyar ta daban,sun manta da duniyar da suke da kuma duk wani abu dake zagaye da su,basa iya tuna kowa da komai sai junansu,burinsu a ko da yaushe su faranta ran junansu. Bayan komai ya wuce sunyi wanka yana shiryata,wayansa tayi k'ara,saurin maida rigan yayi kan bed ya nufi inda phone en ke yashe,MAMA ya gani tana kiran da sauri ko ya d'auka yana karata a kunnensa cikin sallama,amsa masa tayi sannan ta furta "SON kana jina ko.....?" "Ehh! MAMA wani abu ya faru ne..?" "A'a SON ina so ne dai duk abunda kake yanzun ka kawomin BABY gida akwai wani abu dake shirin faruwa..." 'Dan kallo inda take yayi yaga shi take kallo,d'an murmushi yayi mata yana ajiye wayan kan mirror,inda take ya nufa yana zuwa yad'auka rigan ya sa mata,sannan ya nufi cikin closet ya d'auko mata Arabian gown wanda yake da d'an sakewa bazai kuma takurata ba,da mamaki take kallonsa coz ta jima bata fita ba "JAAN ina zamu kuma naga kana shirin samin kaya bayan kasan banson zafi...?" "No JODI zamu gida ne,ban san mene yake shirin faruwa ba,MAMA tace muje yanzun.." Kai kawai ta girgiza masa alamun ta gane,yana gama shiryata shima ya shirya,d'aukanta yayi ya nufi hanyan fita da ita,hannayenta zagaye da wuyansa har ya sanyata a mota,k'ofar ya bari a bud'e sannan ya koma ya kulle gidan,cikin lokaci k'ankani suka iso,shigowa yayi parlour yana d'auke da ita,nan suka tarar da gaba d'aya mutanen gidan a babban palour,sauketa yayi suna bin cikin parlour en da kallo ganin yadda suma ake binsu da kallo,hannunta ya rik'e suka k'arasa ciki suka zauna,sannan suka gaida iyayen nasu dake zaune,suka kuma gaisa da sauran y'an uwan nasu,suka kuma shiga sahun jiran jin me ke faruwa akayi irin wannan taron. SADEEQ BIGGY aka sa ya bud'e taron da Addu'a sannan ABBA ya fara magana yana kallon KHUBRA dake zaune ta mik'e k'afafunta "Al-hamdulillah da Allah ya nuna mana rana da kowannenmu yake cike da farin ciki da kwanciyar hankali,muna k'ara godiya ga Allah daya had'a kawunanmu muke zaune da junanmu lafiya ba tare da wata fitina ta b'illo mana ba,sai dai a yau ina son ku bani aron hankalinku domin a kwai wani al'amari daya ke faruwa wanda cikinku babu wanda ya sani sai mu da muke zaune lokacin da abun ya faru haka kuma kuma wasunku sun sani sai dai da jimawa,amma idan kun saurari bayanin da za ayi yanzun zaku ita tunawa... Da farko dai ke KHUBRA shin zaki iya shaida wad'annan mutanen dake zaune gefe...?" ABBA ta kalla da yake mata nuni da gefe da hannunsa,hannun tabi da kallo zuwa inda yake mata nuni nan ko idanunta sukayi arba da wasu yank'wanannun tsofi mata su biyu d'aya jikinta duk wasu irin k'uraje sun feso mata a jiki saboda uwar daud'a data lillub'esu,kallon rashin sani tayi musu sannan ta kalli ABBA da sauran mutanen cikin parlour'n ta ce "A'a ABBA ban shaida suba." Matan dake zune gefe sai kuka suke kamar wani nasu ya rasu suka kalleta suna sake b'arkewa da kuka mai cin zuciya kowa su yake kallo,da k'yar suka kalleta d'aya tana fad'in "KHUBRA yanzun baki shaidamu ba? tabbas babu makawa mu mun san masu laifi ne a gareki kuma dama babu yadda za ayi ki shaida mu,idan har baki gafarta mana ba to tabbas baza mu tab'a gamuwa da rahama ba cikin rayuwar da zamuyi dama wadda mukayi a baya saboda munyi rayuwa ne cikin k'unci.." K'uresu tayi da ido duk dan ta gane su,amma hakan ya gagara ta kasa bambance kamanninsu. "Ni ce fa MA'U KHUBRA...Dana kawo ki aikatau,wanda tun bayan wanni biyar dana kawoki ban sake waiwayoki b..." Ido KHUBRA ta zare tana kallonta da mamaki shimfid'e kan fuskarta na yadda ta kasa game kammaninta,ko tantama babu d'ayar kam LADIYO ce dan kamarsu d'aya su biyun fun can da. Daga nan MA'U ta kwashe komai daya faru tun bayan data bar gidan,yadda tayi mata asiri kuma cikin hukuncin Allah kasancewar bata da hak'k'i Allah ya kareta,sannan ta d'ora da yadda asirin yayi tasiri akanta ita,maza suka dinga binta itama tana binsu kamar dai yadda igiyar ruwa ke kad'awa gefe zuwa gefe,kaf ta kwashe komai har ciwon da take d'auke da shi a halin yanzun,wanda tun bayyanar cutar a jikinta ta koma gidanta,kuma har lokacin bata bar halinta na biye-biyen maza ba,a haka ne wata rana suna tsaka da aikata masha'arsu a soron gidan nata kawai sai ga wata mak'ociyarsu nan ta shigo da niyyar tambayarta kasancewarta bak'uwa a unguwar,ganin da tayi musu mak'ale da juna yasa ta fasa k'ara dalili kenan daya sa mutanen unguwa taruwa kasancewar da yamma ne kuma ranar babu aiki,da yake an san ba aure gareta ba nan ko aka shiga jibgarsu babu ji bare gani ta k'arasa da fad'in "Da kyar na samu na gudu,daga nan ban zame ko ina ba sai nayi tasha na tafi garin KASHIN DILA gurin YAYA,a lokacin dana je na sameta cikin mawuyacin hali wanda ko abincin da zata cima gagararta yake,babu gurin kwana babu suturar kirki har sai tayi bara take samun d'an abun da zata sawa cikinta,a k'ofar gida cikin rumfa na isketa gidan kuma a kulle,ko dana tambayeta sai take shaidamin cewa MALAM BUBA ya sake ta,kuma gidanma ya sallama shi ga mai gari tare da sauran kadarorin da iyayensa suka bar masa,yayi kuma sallama da mutanen garin da sunan bazai sake dawowaba.Sannan ta sanarmin da KHUBRA kin koma tare da wasu mutane da suka shaidawa MALAM BUBA a hannunsu kike kuma dai da alamun suna da alak'a tsakanin su da shi MALAM en Lamar yadda muka samu labari yanzun,to bayan nan kuma muka ci gaba da zama a garin wahalar da muke ciki tasa muka baro can muka dawo nan gidan dana zauna a nan kano,bayan mun dawo nan mun d'auki lokaci muna zuwa wannan unguwar muna neman gidan dana kawo ki aiki,sai dai Allah bai nufa zan gane gidanba sai yau da muka shigo muna neman taimakon abunda zamu ci saboda duk wata dukiya da nake da ita ta k'are yanzun,sai Allah yasa muka ga matar dana kawoki hannunta.Shi ne ta shaida mana kinyi aure tun shekaru biyu da aula wuce,min nemi son ganinki ne a gurinta shine race my jira zata kira mijinki ya kawo mata ke. Kunji abunda ya faru tun daga rabuwarmu har kawo yanzun ... Parlour'n kowa yayi shiru mamaki game da d'umbin al'ajabi na hali irin na wad'annan mutane da suke zaune duk ya d'aure musu kai,KHUBRA kam zuwa lokacin hawaye sun gama wanke mata fuska banda godiya ga Allah daya kareta ya kuma tsareta daga fad'awa tarko ba tare da an samu damar keta mata mutuncin taba take yi,mik'ewa BB yayi ya kamata suka bar gurin duk maganar da suke yi na ta yafe musu kan cutar da ita da suka yi,bai bari ta tsaya gurinba dan shima da kansa haushinsu yake ji,kuma yayi niyyar d'aukar mataki a kansu sai dai ya tuna wata magana da suka tab'ayi da yake ce mata sai ya d'auki mataki kansu,amsar data bashi a lokacin itace ta sake dawo masa,dalili kenan daya sashi janyeta a gurin coz yana son rarrashinta... 'Dakinsa na da ya shige da ita,d'akin ta kalla da hawaye har lokacin a cikin idonta,yana nan kamar yadda yake da,key ya murzawa k'ofan danma kada wani ya samu damar shigowa,janyota yayi ta shige cikin jikinsa,yana d'an jijjigata har ya samu tayi shiru sai ajiyar zuciya da take,bakin bed ya zauna ya d'orata akan cinyansa yana goge mata fuska,cikin kunnenta yake hura mata iska har sai da ta koma hayyacinta,mik'ar da ita ya sake yi tsaye tayi tunanin fita za suyi,da sauri ta rik'e shi tana sake sakin sabon kuka "JAAN please kada ka mai dani gurinsu dan Allah baran iya zama guri d'aya da suba...kaji..?" "Ok ok..! yi shiru babu inda zamu tunda baki so kinji ko..Zo nan na cire miki rigan kisha iska.." Matsawa tayi jikinsa,sunkuyawa yayi a gabanta ya shiga bud'e mab'allan rigan jikinta,singlet ne a jikinta ta ciki sai nicker's,rungumeta yayi ya nufi saman bed da ita,kanta ya d'ora kan cinyansa ita kuma ta kwanta a gefenta na dama fuskarta na kallon fuskarsa,sai ajiyan zuciya take saukewa,gashinta ya shiga shafawa yana mata magan-ganu masu dad'i da kwantar da hankali,saboda kasancewarta mai d'auke da juna biyu daya tasamma tsufa ba'a son kasancewarta cikin b'acin rai,kafin wani lokaci sai gata ta ware har suna wasanni cike da nishad'i.. Can ko a parlour bayan barin su gurin MA'U da LADIYO sake b'arkewa suka yi da kuka ganin KHUBRA ta bar gurin ba tare da ta yafe musuba,kan irin cutarwar da suka mata,kuka suke suna k'arawa akan a kirata su nemi gafararta,shiru mutanen dake parlour en su kayi sai sauraren su suke sai da suka yi kukan son ransu wannan suka yi shiru, suna kuma dad's tonawa Kansu aspirin abubuwan da suka yita aikatawa Wanda aka sani dama Wanda ba a saniba,cike da tausyawa halin da suka jefa KHUBRA a ciki da mahaifiyarta data jima da rasuwa saboda girman kaidi da suka dinga shiryawa mutanen cikin parlour en ke kallonsu,da kyar UMMI ta bud'e baki tayi magana wanda yasa kowa ya maida kallonsa kanta,hatta kuwa da su masu koke-koken neman gafara,kiran KHUBRA da BB tasa ayi don kawo k'arshen komai,ko da d'an aike KHALEEL yaje ya tarar da k'ofa a kulle baiyi knocking ba ya dawo dan shima akan dole yaje saboda dai kawai bazai iya cewa UMMI a'a bane yasa yaje,sanar mata yayi da k'ofar a kulle take,sashi tayi ya koma yayi knocking ai ko kamar yadda ta umarta haka yayi,bud'ewa BB yayi sukayi ido hud'u da KHALEEL a nan ya coge ya kare k'ofar ba tare daya bawa KHALEEL damar gano cikin d'akinba ya furta "Ya akayi ne...?" "UMMI tana kiranku yanzun..." Badon yaso ba ya koma ciki yana b'ata rai,shi kam babu yadda za ayima ya tasheta tana bacci,saboda haka ya fice had'e da kulle k'ofar,ganinsa shi kad'ai yasa suka kalle shi UMMI tana tambayan KHUBRA "UMMI tayi bacci ne..." Amsa daya bata kenan fuska a murtuke,aikuwa MA'U ta hau sheshshek'ar kuka,BB wani kallo ya jefeta dashi daya sata shiga nutsuwarta tana sunkuyar da kai k'asa,babu yadda basu yiba akan a tasota ta yafe musu,shi kuma ya kafe akan wallahi babu abunda zaisa ya tasheta,kawai suje an yafe musu saboda ubangiji yana son masu yafiya kuma itama zata yafe musu in sha Allah su tafi kawai,k'in tafiya suka yi ganin sun matsa kan sai sun nema yafiyarta su da ita kuwa yace musu idan suka takura to wallahi zai janye yafiyar da aka musu. Babu b'ata lokaci suka fice suna kuka had'e da waiwayen gidan dan sun san shi kenan kuma suda sake ganin KHUBRA bare kuma MALAM BUBA daya koma AL-HAJI ABUBAKAR,wanda yake ji da dukiya a yanzun,ta inda cikin shekaru biyu da watanni ya bawa wasu miliyoyi baya. *WAIWAYE....* Tun bayan lokacin da MALAM BUBA ya kori LADIYO daga cikin gidansa,yayi sallama da mutanen garin,nan ya saida duka wata kadara daya mallaka ya tattaro kan dukiyarsa,wacce a k'arshe bayan dawowarsa ya damk'ata a hannun ALHAJI SAFWAN,inda shi kuma ya kawo shawara suka had'a kai su uku suka sake bud'e wani company da yanzun yake k'ark'ashin jagorancin KHALEED da KHALEEL. _Wannan kenan....._ Bayan tafiyarsu aka koma maida labarin yadda al'amura suka faru a baya,kowa sai jimami yake kan yadda abubuwan suka faru.Bayan komai ya lafa su ABBA suka koma bakin aikinsu a d'ayan company ensu. Su kuma sauran yaran aka barsu nan suna ci gaba da hiran haihuwan KHUBRA nan da wani watan suna kuma ci gaba da tsara irin shagulgulan da zasu yi idan ta haihun............ *ONE MONTH LEAP...* KHUBRA ce kwance saman gado na majinyata masu haihuwa sai juya kai take gefe wasu nurse's na turawa daga kusa da kanta kuma BB ne yana ta faman shafa mata kai yana jera mata sannu cike da tashin hankali,har aka shiga da ita labour room en,sannan aka kulle yana waje bakin d'akin sai safa da marwa yake. Tun yana kallon mintuna da suke shud'ewa kuma yana kallon k'ofar d'akin da aka shiga da ita,har hour guda yayi ba tare da an fito da itaba,daga hour d'aya aka tafi da rabi,sannan biyu,uku,hud'u,ganin abun bana k'are bane kuma hankalinsa na kanta gaba d'aya nutsuwa tayi masa k'aura,burinsa bai wuce sanin halin da take cikiba. Wata nurse ce ta lek'o,jin an bud'e k'ofar yasa shi nufar gurin da sauri. "Kaine JAAN ko waye nema ohooo...?" Bai bata amsaba ya janyeta gefe had'e da shigewa,kallo ta bishi da shi ganin ya shige babu magana,bakin gadon ya nufa ganin cikin awanni hud'u da shigowarsu babu wani abu daya canja,duk ta gama galabaita,hannunta ya rik'o cikin nasa,idanunsa lokaci guda ganin halin da take ciki har sun gama sauyawa zuwa jaa,su kuma nurse's en sai faman damunta suke kan tayi nishi amma ina babu k'arfin yin hakan a tare da ita,gaba d'ayama sun gama bashi haushi kan tsayawa da sukayi suna b'ata lokaci tun d'azun kuma har lokacin babu sauyin da aka samu tun da suka shigo da ita,hannun long sleeve ensa ya nad'e cikin b'acin rai yace su bashi guri tunda basu san aikin suba,cikin ya shiga d'an dannawa a hankali kamar dai yadda akema masu ciki idan zasu haihu,yana kuma fad'a mata kalmomin da zasu bata k'warin guiwa,matsawa ya sake yi dai² bakinta ya sanya nashi ganin yadda take kwance tana sauke numfashi da kyar,iska ya shiga hura mata hannunsa d'aya na kan cikin yana ci gaba da daddanawa a hankali. Cikin y'an mintuna da shigowarsa ta samu d'an k'warin jiki,nishi mai k'arfi yayi escafe a tare da ita,wanda ya bawa kan jaririnta damar fara fitowa,da sauri nurse's en suka matso,da taimakon Allah sannan da nasu taimakon suka janyo jaririn,cikin y'an mintuna ta sake sabon yunk'urin wani nak'udan take wani sabon jaririn ya sake kunno kai,a tak'aice dai sai da aka zaro jarirai uku daga jikin KHUBRA. Ko ta kan jariran bai biba,in da matarsa take ya nufa yana jera mata sannu da Santa mata albarka,itako sai maida numfashi take da kyar Dan da ganinta ko ba a fad'a ba kasan ta sha wahala,duk jikinta yayi sweat en wahala,mouth to mouth ya shiga sake mata ko dan ta samu daidaituwar numfashi............. *COMMENT FOR MORE PAGE'S.......* 💃💃💃💃💃 *~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~* *_®єαl $mαѕhєr._* 😉 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/ SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVEL'S GROUP@web.facebook.com *©®2018* *10/ɑմցմՏԵ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~___________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ 6⃣4⃣ *SECOND TO THE LAST.* *BIGGY* kuwa tun bayan daya samu aiki a revenue office,wato ofision tattara haraji,ya daina wani aiki da yake a baya,wanda ba k'aramin mamakinsa yaransa suka yiba na ganin chanji lokaci d'aya a tare da shi,da farko sun ci gaba da zama cikin gidan nasa sai dai kuma daga baya lokacin da zai yi aure kuma har lokacin akwai wasu halayya nasu da basu dainaba,dalili kenan daya sashi yanke shawaran rabuwa da su dan kada wata rana su janyo masa bala'in daya fi k'arfinsa. Wata rana bayan ya zaunar dasu a parlour nan ya shiga yi musu nasiha yana janyo musu ayoyi da hadisai cikin abunda Allah ya sanar da shi na daga ilimi,jin ruwan ayoyin daya ke janyowa wanda suke tsoratarwa zuwa ga masu aikata halaye irin nasu dama wasunsu da kuma narkon azaba da aka tanada ga mai aikin yasa su kuka,basu tashi a gurinba sai da sukayi masa alk'awarin in sha Allah suma sun daina,yayi farin ciki sosai da hakan ya faru,nan yake shaida musu zaiyi aure nan bada jimawaba suka masa fatan sanyawar alkhairi,tun daga nan ya sallamesu da kud'ad'en da yasan idan har sun rabu cikin su babu wanda zuciyarsa zata kawo masa d'aukan abun wani ko kuma su koma irin waccan rayuwar.Tun da suka yi sallama da shi a lokacin ya musu fatan alkhairi shi kenan basu sake had'uwa ba,shima bayan sun bar gidan ya shiga parking kayansa,dillallai ya samu sukayi cinikin gidan da kayan gidan gaba d'aya,take ko ya sai da shi da komai daga shi sai kayan jikinsa ya fito daga gidan,ko bayan ya bar gidan ya d'an kwana biyu a hotel sannan daga baya ya samu wasu dillallan suka samo masa gida a wani unguwan daban,nan BIGGY ya koma da rayuwarsa,wanda kuma nan ne aka kai masa amaryarsa wato ASHNA wacce a yanzun take MAMA ga d'ansu MUHAMMAD AL'MUSTAPHA.... 《《》》 *INA LABARIN BOKA...??* BOKA kuwa tun bayan da LADIYO ta masa wannan gani a ranar da MALAM BUBA yayi musu mugun kamu bai sake dawowa gurinta ba dalilin da yasa kuwa hakan ta faru shi ne,a lokacin bayan ya bar gidan LADIYO daga nan wani gari ya wuce wanda a wannan garin akwai wani malami mahaddacin al-k'ur'ani,tun da Allah yasa wannan bawan Allah yayi aure da matarsa d'aya wacce take fitinanniya tun tana yarinya kamar su LADIYO,tun bayan aurensu data ga ba irin wanda za tayiwa duk abunda ranta ke so bane yasa ta shiga bin malamai y'an tsubbu da bokaye duk akan tana neman abunda zata malakke shi,sai daifa hak'anta yak'i cimma ruwa sakamakon shi wannan bawan Allah ako da yaushe zaka tarar da shi cikin alwala kuma yana tilawar al-k'ur'ani,a biye-biyenta ne suka had'u da BOKAN su LADIYO,wanda a ranar da MALAM BUBA ya gansu bayan ya bar nan bai zame ko ina ba sai gidan wannan malami daya fita sallar asubah kasancewarsa limamin garin nasu,kamar ko wane lokaci bayan an idar ya zauna tilawa nan a k'ofar gidan nasa yana cikin karatu,almajiransa da sauran datijjan garin masu sha'awar neman karatu suna zaune nan gaba gare shi a haka har gari yayi haske sosai.. Can ko a gidan MALAM lokacin matarsa na tsaka da bacci gari har yayi haske tana ta faman bacci bata saniba bare ta tashi ta gaida mahalicci,zuwan bokan shi ya tasheta wanda tana yin arba da shi tayi dariya kasancewar dama sun saba,haka suka shiga aikin gabansu kamar kowane lokaci.K'arfi,mu'ujiza da girman kalmomin da ake karantawa k'ofar gida suka fara tasiri cikin gidan malamin wanda suka yi sanadiyyar daya janyo jikin boka cikin lokaci k'ank'ani ya fara hayak'i,faruwar hakan ke da wuya matar malam ta daka tsalle had'e da ingije shi daga kanta ta fice a guje daga d'akin,a tsakar gida ta tsaya tana raba ido tunawa da irin hukuncin da za a mata a garin idan har aka san abun da ta aikata yasa ta fashewa da kuka dan kam muddin malam ya sani tofa lallai ne jefeta za ayi da ranta har sai ta daina motsi kuma mutane salihai ba za su mata jana'iza ba,wannan dalili yasa ta k'ara k'arfin kukan nata,babu b'ata lokaci ta jaa mayafinta ta fice da gudu a gidan saboda wani tunani da tayi na bar in garin tun kafin asirinta ya kaiga tonuwa,mutanen dake k'ofar gidan da suka ganta a haka suka bita da kallo ganin yadda take gudu iya k'arfinta,mamaki duk ya cika musu zuk'ata,tana cikin gudun ne kuma Allah ya kawo wani mai akori kura take ya banketa,dalili kenan da ko shurawa ba tayiba nan take rai yayi halinsa tace ga garinku nan sanadiyyar fashewa da kanta yayi wannan shi ya zama k'arshenta. Shi ko boka a k'alla sai daya kwana biyu cikin d'aki ba asan ya mutu ba jikinsa har ya fara tsutsa,mugun warin da malam yaji shi yasa shi nufar d'akin sai dai warin ya wuce tunaninsa,da k'yar dai aka samu aka bud'e d'akin wanda aka fito da gawar boka dake kwance kan gadon matar malam,had'awa akayi da katifar gaba d'aya aka fito da ita,sai a lokacin mutane da dama suka fuskanci dalilin daya sa matar malam take gudu waccan ranar,tasan abunda ta aikata shi yasa ta nemi guduwa,to yanzun dai ga abunda Allah ya nufa dasu duka babu wanda yake raye... _Wannan kenan,su boka an tafi ga kuma yanda Allah yayi k'arshensa ya kasance dama wasu daga magoya bayansa...Allah ya karemu daga mummunan k'arshe._ 《《》》 *INA LABARIN TABAWA K'AWAR LADIYO...???* Tun bayan da LADIYO tayita zuwa gidanta akan tana neman taimakonta lokacin da take son neman MA'U a waya,a wani yammaci bayan zuwanta gidan lokacin suna zaune tsakar gida sai ga mijin TABAWA nan ya shigo,kamar ko wane lokaci nan TABAWA ta bud'e ido da murya iya k'arfinta zata fara zuba masa rash in mutunci Lamar yadda ta saba,take bata ko k'arasa fad'in abunda tayi niyyaba ya d'auke mata fuska da mari ganin yadda taci kwalarsa sannan ya shiga kora musu daga ita har LADIYO'N,kuma ya k'ara da cewa daga ranar kada ya kuskura ya k'ara ganin k'afar LADIYO a gidansa,duk kuwa ranar daya sake ganinta to ko shi kad'ai yasan me zai musu. Tun daga ranar LADIYO bata sake yunk'urin zuwanba,dan dama mijin na TABAWA mugun masifaffe ne,dalilin sakkowar tasama kuwa ya had'u da k'arfin asirine. Bayan tafiyar LADIYO ya zauna ya wanke TABAWA tsaf sannan ya k'ara mata da cewa zai yi aure idan kuma har ta sake ko da kallon banza tayi wa matarsa to ta kuka da kanta. Ko bayan da yayi aurenma,ko kad'an TABAWA bata da wani power a gidan,hasalima ko k'ofar gida ya hanata zuwa bare ta shiga mak'ota,rayuwa tayiwa TABAWA k'unci a gidan mijin nasu,wanda ta koma tamkar baiwa a gurin uban gidanta,haka ta koma duk wani aiki na cikin gidan ya dawo kanta bata da sauran katab'us.... _Hattara ga masu hali irin nasu TABAWA,LADIYO,MA'U,BOKA,MATAR MALAM da sauransu,kunga dai yadda k'arshensu ya koma mask iron wannan hali tun kafin damar Ku ta kufce ya kamata kuyiwa kanku fad'a had'e da gyara tsakaninku da mahalicci dan duk Wanda ya mutu a haka Allah kad'ai ya barwa kansa sanin iron hukuncin da zai maka,Allah ya tsare my kuma ya tsare mana imaninmu..Ameen._ 《《》》 Kasa fita yayi daga labour room en yana nan rik'e da matarsa,inda yabar yaran hannun nurse's suna gyara su,cikin wahalalliyar murya na mutumin daya galabaita ta kalleshi da idanunta dake lumshewa suna bud'ewa,murmushi kawai yake zuba mata. "JAAN MAMA fa da UMMA...?" Ido ya fiddo waje dan sam yama manta da batun ya sanar musu,kansa ya dafe yana birkita gashinsa,alamun data gani kenan a tare da shi ta gane babu wanda ya sanarma. "JODI...Basu saniba,ni kuma na manta ma da ya kamata ace na sanar musu.." 'Dan murmushin k'arfin hali ta masa ta sake lumshe idanunta,aljihunsa ya laluba da niyyan d'aukan waya ya kira su,sai dai wayam babu wayan,sai a lokacin ya tuna da bai d'aukoba,lower lip nasa ya cije tunawa da kayan dake shirye cikin d'an akwatin kawai ya d'auko shima kuma suna motan bayan su kuma bai d'auko wani abuba. "Ya Allah...! Komai ma na manta daya kamata nayi..JODI wait a minute....I will be back right now.." Yana fad'in haka ya mik'e had'e da bata fake a cheeks enta na dama,cikin sauri ya fice ya nufi mota,kayan ya d'auko ya dawo had'e da bawa nurse's en ya shaida musu zai dawo nan bada jimawa ba in sha Allah,daga haka ya fice cike da sauri yayi starting motan,direct daga nan gidan UMMA ya fara zuwa wato HAJIYA ZUWAIRA,tana ganin yana yinsa ta fahimci da akawai abunda yake faruwa,ganinsa sai murmushi yake zubawa yasa ta itama tayi murmushin tana fad'in "Kada dai ka ce KHUBRA ta haihu...?" Aiko dariya ya sake yana fad'in "Haka ne UMMA'NMU...Yanzun ma na barota hospital,so saboda ba waya a jikina yasa ban samu na kira kowaba,yanzunma gida zanje na koma.." Da murna sosai take godiya ga Allah bisa ni'imar da yayi musu,sallama yayi mata ya fice ita kuma nan ta d'auka waya tana kira ABBA ta shaida masa,a lokacin ko suna tare a office d'in ABBA SAFWAN suna tattaunawa akan wasu kaya da zasu fitar sak'on ya iske su,cike da farin ciki ta sanar masa,aiko shi kansa tasa murnar kasa b'oyuwa tayi dan yadda sak'on yazo masa a lokacin sai yaji kamar lokacin IYA ke sanar masa da k'aruwar KHUBRA da ya samu,wasu hawayen farin ciki ya goge inda yake tambayarta me aka samu.Shiru tayi tana fad'in "Tabbb! kaga kuwa abunda ban tambayaba kenan,kuma har ya tafi dan sauri yake lokacin daya zo,ya sanarmin ita kad'ai ce sai likitocin daya bari suna gyara su..." Murmushi yayi na farin ciki sosai ya furta "To babu damuwa in sha Allah yanzun driver zaizo gida sai kije gurinta kafin mu k'araso.." Daga haka suka yi sallama ya kashe,yana kuma shaidawa su ABBA dake jiran ya gama,sun ga yana goge hawaye d'azun,ko da ya basu labarin abunda ya faru,su kansu murnansu da farin cikinsu kasa b'oyuwa yayi,tattara duk abunda suke sukayi da niyyan tafiya asibiti ganin jikokin nasu da basu san me aka haifa ba har lokacin.. Cikin d'an lokaci kad'an har labari ya gama zagaye dangin na haihuwar KHUBRA a yinin ranar ta jumu'ah. Kafin wani lokaci mai tsawo har d'akin asibitin ya gama cika da iyaye da y'ay'a na gidan,kowa ka kalla kasan yana cike da farin cikin k'aruwar da aka samu na yara har uku sukutum a ranar.Maijego kuwa duk wannan budurin da ake bata sani ba tana ta faman baccin wahala dan kam ta galabaita ba kad'an ba,yara da suka zo da farin jini kowa burinsa ya d'auke su. Daga KHUBRA har yaranta sun sha addu'ah a bakin y'an uwa da abokan arziki,haka mai jego taci gaba da samun kulawa a nan asibitin saboda k'in sallamarta suka yi duba da irin wahalar data sha kafin haihuwar,kwananta biyu aka sallameta inda UMMI ta tafi da ita dan bata kulawa ita da jariranta uku,biyu maza d'aya mace kuma ita ce k'arama cikinsu. Gidan UMMI ya koma gurin zuwan BB kullum yana can mak'ale da yaransa da kuma y'ar matarsa,wani lokaci har sai UMMI ta gaji da shi ta kora shi dan kam ba wata kunyar UMMI yake jiba kuma dalilin daya sa aka maido da KHUBRA gidan sun san idan a gidan MAMA take zai iya komawa gidan ya tare.Sai dai kuma nan enma bata canza zaniba,kullum nan yake yini,da k'yar UMMI take korashi idan ko ya fice tofa bashi da gurin zuwa sai dai ya wuce gurin aikin nasu data tashi kuma nan zai dawo ya sake rashewa,a haka har aka shafe tsawon kwanaki shida,wanda zuwa ranar yara sun riga da sun amsa sunansu,HASSAN ya amsa sunan ABDULLAH suna kiransa da ABDUL,sa HUSSAIN da aka rad'awa ABUBAKAR shi kuma suna kiransa da SADDIQ ensa,ita kuma macen da take k'arama ta amsa sunan KHADIJATUL-KHUBRA wato sunan mahaifiyarta,kowa tambayar BB dalilin yin hakan yake,shi ko gogan cewa kawai yake haka yaga dama coz shi ba shi da niyyan sa sunan iyayensu,salon haka kawai wata rana a gaban idonsa a kira masa sunan iyayensa a zaga,KHUBRA kuma da aka tambayi dalilin da yasa ya sanya sunanta murmushi yayi sannan ya basu amsa da cewar "Itace wacce nafi k'auna...Shi yasa na maida sunanta akan y'armu ta fari,kuma ko bayan haka sunan matar Manzon Allah ce ta fari (S.A.W)..." Haka aka ci gaba da shirin hidimomin da aza gudanar a gobe na suna idan Allah ya nufa.... *RANAR SUNA...* Tun da asuba bayan an idar da sallah aka sake jadadda sunayen yara kamar yadda suke,ABDULLAH,ABUBAKAR AS-SADDIQ sai kuma NANA KHADIJATU. FATAHIYYA zaune ta tasa yaran a gaba dan tun da aka dawo da KHUBRA gidan UMMI itama ta dawo nan ta tare cikin shekaru biyu duk wanda ya kalleta sai yayi mamakin girman data k'ara ga class na musamman ba kamar daba da ba wani wayewa gareta ba. Anyi taro lafiya wanda ya amsa sunan taro ba wai taron da yake na muna taroba,inda a ranar BB sai daya bawa mutane mamaki kan irin bajinta da yayi na kyaututtuka daya dinga bajewa ga abar k'aunarsa,duk kuma kan irin farin cikin data sashi a zamansu,haka taron suna ya watse da kyaututtukan da aula samu daga gurin y'an uwa da abokan arziki,haka taro ya watse inda aka bar mai jego da yaran hannun UMMI suna sake karb'ar gyara da kulawa.... Agogo juyi yake inda a kowane motsawar second sai kaga ci gaba ta wani bigire na daban a rayuwa,cikin kwanaki arba'in da haihuwar KHUBRA yara sun dad'a wayo musamman mazan da dama tun a haihuwarsu sunfi LITTLE KHUBRA girma. Tun da safe a ranar kwana na arba'in en ne,BB ya kafa ya tsare a gidan UMMI jira kawai yake UMMI ta bashi approval na tafiya da iyalinsa,tun data ganshi tasan abunda yake nufi,nan ko ta had'e girar sama dana k'asa ta kuma k'i ce masa komai,tun safe har dare yana nan,ganin babu magana makamanciyar ya d'aukesu su tafi yasa ya bawa kansa hak'uri,kallon agogo yayi yaga yadda dare yayi cikin sanyi murya yace "UMMI zan tafi..." Bud'ar bakin UMMI tace masa "To ka gaida gida ko..." Shiru yayi kansa a k'asa ya rasa me zai ce mata,ita kuma tana kallonsa duk abunda yake sai dai bata k'ara maganaba daga haka,kamar zaiyi magana kuma sai ya fasa,cikin sanyin jiki ya mik'e ya mata sallama fuskarsa cike da damuwa ya tasamma hanyar fita daga parlour'n,har ya isa bakin k'ofa sai kuma ya bata tausayi tasan dai ita da kanta yayi hak'uri tunda bai tab'a tambayarta akan zai tafi da ita ko makamancin hakaba,dakatar dashi tayi tana kiransa,dawowa yayi kansa a k'asa dan ji yake kamar yayita kurma mata ihu ko Allah zaisa ta bashi matarsa,hak'uri kam yayi shi har yana neman ya gagare shi. "Zauna nan...Ina zuwa.." Abunda ta fad'a kenan ta mik'e ta shige ciki,y'an mintuna da basu haura talatinba ta fito rik'e da hannun KHUBRA data sha ado cikin wani rantsatstsen less mai kalar sea green sai yarfan duwatsu kalar gold,tana ta fana shek'a k'amshi,fuskarta tasha light make-up tana zuba murmushi ta cikin mayafinta daya rufe mata fuska,dan dama a ranar kam tun da yazo UMMI bata bari ya ganta ba,sai dai y'ay'ansa da yaketa faman yiwa wasa,idan ya d'auki wannan ya ajiye ya d'auka wannan,sai dai da gani kasan LITTLE KHUBRA ta musamman ce a gurinsa... Fuskarta a lullub'e da mayafinta kalar duwatsun kayanta da plat shoe a k'afarta,a hankali har suka iso gabansa,idanunsa tun da suka fito yake kansu bakinsa yak'i rufuwa saboda tsanamin farin ciki har tsaye ya mik'e bai saniba,hannunsa UMMI ta kama ta d'ora na KHUBRA aciki ta damk'e a nata,cikin sanyi ta d'an yi musu tak'aitacciyar nasiha sannan ta k'ara da fad'in cikin zolaya tana dariya "To SON ga matar ka nan na baka....Allah yasa ba a soma fushi daniba.." Dariyar shima yayi sannan ya rungume UMMI yana fad'in "Na gode sosai UMMI'NMU Allah ya biyaki da mafificin alkhairin sakamako.." Duka suka amsa da amin,sannan ya d'auki yaransa biyu UMMI ta d'auko LITTLE har bakin mota ta rakasu,inda KHUBRA ta zauna sannan UMMI ta d'ora mata LITTLE kan cinyanta tana fad'in "To Allah ya tsare hanya,ya kuma karemin ku daga sharrin abun cutarwa...Sannan kuma idan Allah ya kaimu cikin satin nan zansa a nemo y'ar dattijuwar da zata na taimaka miki...Kinji ko DOUGHTER..?" Godiya suka mata sosai mayafin KHUBRA lullub'e har lokacin a saman fuskarta,tana tallafe da y'arsu dake bacci sai k'amshi na musamman yaran keta zubawa kamar iyayensu.Sai da taga tafiyarsu sannan ta koma cike da farin ciki a zuciyarta mara misaltuwa. Suna fita a get en gidan yayi parking gefe,jin ya tsaya yasa KHUBRA murmushi dan kam tasan Ogan nata yau sai yadda Allah yayi da su,tasan babu batun hak'uri a lamarinsa yau kam.Tana cikin tunani taji ya d'age mayafin kanta,da sauri ta kulle idanunta tana murmushi,murmushin shima yayi sannan ya d'auke LITTLE daga saman cinyanta,kanta ta jinginar jikin kujeran tana sauke numfashi a hankali,kusa da y'an uwanta ya kwantar da ita a back seat,sannan ya janyo KHUBRA dake mak'ale jikin kujera kamar idol. Idanunta dake kulle ya kalla yana sakin murmushinsa mai tsada kamar idon nata a bud'e yake,kissing pore head enta yayi sannan idanunta,a hankali ya gangaro saman lips enta,sun jima a haka inda ta samu ta k'waci kanta da k'yar tana mai da numfashin wahala,shi kansa gogan da k'yar ya samu ya daidaita gudun numfashinsa lokacin kad'an har ya tsinci kansa cikin wani duniya na daban,fizgar kan motar yayi yana ta faman murmushin da na kasa gane ma'a narsa...... 《《》》 *GIDAN KHALEEL.* Tun a wayewar garin ranar da KHUBRA take da kwanaki arba'in da haihuwa ZUHRA ta tashi da matsanancin zazzab'i mai zafin gaske,hankalin KHALEEL idan yayi dubu ya tashi saboda yadda jikinta yake ga amai da taketa fama da shi,yini guda har ta fita a hayyacinta,tausayinta duk ya cika KHALEEL,yana nan zaune rik'e da ita a jikinsa DR yazo,ko bayan da aka dubata DR ya gama y'an bicikensa nan ya tabbatarwa da KHALEEL tana da shigar ciki na kimanin wata uku da sati guda,murna gurin KHALEEL kamar zaiyi me dan dad'i. Sai dai kuma wani abu cikin na ZUHRA da alamun mai wahalarwa ne,dalilin daya sa KHALEEL ya yanke shawarar tattara musu y'an kayan da zasu buk'ata,ya tattara ta suka nufi gidan UMMI.. Tafiyar su KHUBRA kenan babu jimawa motarsu ta kunno kai gidan,lokacin har UMMI ta gama shirin kwanciya kenan sallamarsu tasa ta fito. Ganinsu a lokacin harda luggage's ta saki baki tana kallonsu.Bayan sun gaisa KHALEEL ya mata bayanin komai,murna gurin UMMI harda taka rawa saboda zata sake jin kukan jinjiri daga tsatsonta a karo na biyu duk da a yau ta rabu da wasu jariran sai dai fa wannan na musamman ne a gareta... _Toh ZUHRA fatan Allah ya raba lafiya..._ 《《》》 *INA LABARIN HAJIYA LAURA....??* Nasan da yawa kuna da son jin yaya ta kasance a b'angaren HAJIYA LAURA.... Tun bayan da ta san illar abunda ta aikatawa HAJIYA MURJA da labari ya iskota da kuma rashin lafiyar ita HAJIYA MURJA'N,nanfa ta ttara inata-inata ta,duk wani abu na kud'i ta sai da shi da yake dama gidan na HAJIYA MURJA ne cikin abunda ABBA ya bari kafin ya bar k'asar,ta fice ta bar gidan da shirin tserewa k'auyensu,tana cikin tafiya da y'an kayanta cikin wata jaka,har Allah ya kawo ta tasha,cikin ikon Allah,tsautsayin ya afka mata a lokacin da take k'ok'in tsallaka titi,tana tafiya ba tare da ta kula da tahowar motarba,shi kuma mai motar shima baiga lokacin data shigo ba,take ko ya kad'eta kuma ba tare da ya tsayaba kasancewar a lokacin danja ta bawa gefensa hannu ya manni motarsa,suma HAJIYA LAURA tayi yashe a gurin wanda mutane suka samu suka maidata gefen hanya,taimakon gaggawa suka fara bata.Kafin daga bisani akayi asibiti da ita wanda likitoci suka shafe tsayin lokaci suna bata taimako. Tsawon kwanaki biyu ta shafe a sume ba tare da tasan halin da take cikiba,sannan a kwana na uku ta farfad'o tana ta fana surutai kamar zararriya,da kyar likitoci suka samu suka shawo kan matsalar tata,sai dai fa wani abu HAJIYA LAURA duk k'ok'arin likitocin sun kasa hanyan da zasu tashi k'afarta,wanda a sakamakon had'arin HAJIYA LAURA ta rasa k'afarta d'aya da hannu. Wannan abu ba k'aramin tada mata hankali yayi ba lokacin data koma hayyacinta,tayi kukan har hawayenta sun dena zuba,sai daifa tana nan da damuwa fal a ranta na rushewar lamarinta,haka dai take ci gaba da karb'ar kulawa daga malama'n asibitin kasancewar na gwamnati ne,batun magani kuwa sai dai idan Allah yasa sun samu kud'in dubiya daga gurin masu zuwa ziyara,idan kuma Allah yasa ta samu en sai ta samu ta fanshi magani da shi Wanda shima jimawa zai k'are....Abinci kuwa ba a maganarsa ma saboda bata da wanda zaiji k'anta ya d'auki d'awainiyar bata ko wane lokaci,bare kuma ayi maganar d'an jinya,wani lokacin sai dai ko a nan gadajen kusa da ita da suke tausaya mata su sanmata,a haka har Allah yasa ta shafe tsawon shekara guda a asibitin Wanda ba tare da an sallameta ba ta tsere. Bakin danja ta samu nan take bara ta samu abunda za taci,tana yawo da sanda wanda ke taimaka mata tana tafiya,tayi bak'i ta rame bayaga kod'ewa da tayi wahala kullum k'aruwa take a kanta,kullum ta tuna abunda ya faru da ita sanadin rasa k'afar da tayi sai tayi kuka,ga dukiyar data tattara zata gudu tun da tayi had'arin bata sake ganin jakar tataba... A kullum burinta a yanzun bai wuce zuwa neman gafarar HAJIYA MURJA ba sai dai tsoro ya hanata tunkarar gidan hajiyar.A haka har aka sake shafe shekara guda da fitowarta daga asibitin,kuma har wannan lokaci bata tara kud'in da a ganinta ta wannan hanyar zasu tarunba.K'ark'arinta ta samu abunda zata sai abinci ta ci.Gurin kwana ko ya zame mata abu mafi wuya ya kasance yanzun HAJIYA LAURA dake da d'akunan bacci iri daban daban yanzun sai dai bin rumfunan kasuwa........ *Alhaki kuikuyo kenan jama'a ga dai yadda k'arshen HAJIYA LAURA ya kasance,ta manta a sanadiyyarta ta jefa y'ay'a da dama cikin halin da yafi nata muni,tasa su kwana bakin kasuwa,da yawon neman abunda zasu rufawa kawunansu asiri tamkar mabarata,cikin garin da basu da kowa kuma basu da komai,ta manta da had'arin dake cikin bar in y'ay'ata mata a gaban iyayensu,wanda hakan dai² yake da siyan lasisin tarwatsa musu rayuwa..Duk ta manta da haka ta kuma toshe kunnuwanta a lokacin... Huh!!...Allah ya k'ara rufa mana asiri duniya da lahira..ameen...* *COMMENT FOR MORE PAGE'S..........* 💃💃💃💃💃 *~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~* *_®єαl $mαѕhєr._* 😉 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/ SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVEL'S GROUP@web.facebook.com *©®2018* *11/ɑմցմՏԵ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~___________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ 6⃣5⃣ *LAST PAGE.* *I* sowarsu gida cikin mintunan da basu gaza arba'inba,ya fara bud'e mata k'ofan ta fito sannan ya bud'e back seat ya d'auko LITTLE dake bacci,mik'a mata ita yayi har lokacin yana sakin murmushi mai kashe jikin mai kallonsa,akan shoulder enta ta sata sannan tayi gaba,ABDUL da AS-SADEEQ ya d'auko ya d'ora su kan shoulder's ensa sannan ya tura k'ofan da k'afarsa,sai da ya tabbatar da ya kaisu har bed room ya kwantar da su,sannan ya koma don shigo da kayansu dake cikin booth. Zama tayi gefensu tana kallon yadda yaranta suke k'ara girma,baccinsu suke hankali kwance kasancewar yaran basu da wani rigima shi yasa lokuta da dama ko a gidan UMMI ita kad'ai take kwana yaran kuma zaka tarar suna tare da UMMI.A nan ya sameta ta k'ure yaran da kallo cike da sha'awa da soyayyarsu,shigowarsa yasa ta kai dubanta gurin daya ke ajiye luggage set en nasu,ganin ita yake kallo yasa ta sakar masa murmushinta dake k'ara haske zuciyarsa,cikin d'an k'ank'anin lokaci ya k'araso gabanta,kusa da ita ya zauna yana sakin sanyayyar ajiyar zuciya,hannunta daya sha zanen henna ya d'ago yana kallo,sosai henna en ya masa kyau,kallonta yayi da alamar tambaya a fuskarsa ita kuma sai kawai tayi y'ar dariya tana fad'in "UMMI tasa akamin d'azun..." 'Dan tak'aitaccen murmushi yayi yana kai hannun nata saitin bakinsa,kiss ya sakar ma hannun nata wanda ya haddasawa KHUBRA mutuwar jiki lokaci guda,idanunta ta lumshe tana sakin siririyar ajiyar zuciya,hayewa yayi ya kwanta kan bed en kansa na kan laps nata,ita yake kallo har lokacin bakinsa da magan-ganu masu girma sai dai yanzun kam ba lokacin yinsu bane,shi kad'ai sai sakin smile yake,idan ya juya ya kalleta ya sake juyawa ya kalli kid's ensu wani farin ciki ne mak'are a cikin zuciyarsa wanda ba shi da limit,mayafin data k'i cirewa tun shigowarsu ya kalla yana murmushi "Yaushe kika zama matar liman kam....?" Tambayan ya zo mata unexpectedly,sai dai data kalle shi kasa fad'in komai tayi,niko a raina nace ko dai KHUBRA bakin ya mutu tun a labour room ne..? Ganin bata kula shiba yasa ya mik'e da sauri kamar ana fizgarsa,mayafin ya d'auke daga jikinta sannan ya sake komawa muhallin da yayiwa kansa ya kwanta,hannunta da yayi mata nauyi ta d'ora saman curly hair nasa da yake a gyare tsaf,ba kamar na samarin wannan lokacinba da za kuga yayi cukui² abun k'yama tana birkitawa,idanunsa ya shiga lumshewa dan dad'in abunda take masa a kansa yake ji kamar tana masa susa a kan,sun d'an jima a haka kafin ya mik'e yana fad'in "JODI muyi wanka...ina jin bacci..." Ita dai kawai ta kad'a masa kai amma magana tunda suka kamo hanya gaba d'aya kafafen sadarwa na bakinta suka tafi yajin aiki,kallonta kawai yayi da mamakin meke damunta kuma yau ta zama wata so speechless,k'ok'arin cire mata kayan ya shiga yi da sauri ta dafe tana kad'a masa kai,still yayi yana kallonta kuma bai fasa abunda yake niyyaba,kuka ta fara wanda sheshshek'ar kukanta yasa shi kallonta da matuk'ar mamakinta,yau kuma shi ne take yiwa kuka kan zai cire mata kaya to ko mene take nufi,hannunsa ta rik'e tana kad'a masa kai alamun bata so,har lokacin bai daina mamaki ba kallonta ya sake yi yana fad'in "Me yake damunki kuma yau...?" Shiru tayi masa kuma bata bar kukanba har lokacin,bai fasa tambayartaba yaci gaba dan ya kasa ganema kanta a yau kam,cikin sark'ewar murya wacce take cike da tsoro ta furta "Ka bari zan iya da kaina...." "Bakya so ne na cire miki kayan...?" Kai ta d'aga masa alamar ehh "Ok!....Shi kenan.." Rabuwa yayi da ita cike da b'acin ran abunda tayi masa,kenan duk rawar k'afar da take akan d'ebosu ya tashi a banza ko me?? shi kam sam ya kasa gane nufinta,mik'ewa yayi yabar inda take amma sai yaga ko a jikinta wait an tsikari kakkausa,ficewa yayi inda yayi mata banging k'ofan,d'an tsorata tayi wanda a sanadin haka yasa LITTLE motsawa,sai dai Allah ya taimaka bata tashi ba,wani marayan kuka ta saki,cikin kukan take fad'in "Wayyyoo! Allah shi kenan na jawowa kaina..Da na san ban masa haka ba,yanzun yaya zanyi...?" _Niko nace mata ke kika sani kuma..._ Kukanta taci gaba da yi tana nan zaune ta sa yaran a gaba tana kallo hawaye na ci gaba da sauka akan fuskarta,yarfe hannayenta take zuwa can taci gaba da fad'in "Ni dai gaskiya baran iya biye maka ba,haka kawai daga haihuwan nawa naje ka sake bani wani,dubifa duka shekaruna nawa amma da yara har uku,ni wallahi baran iya sake haihuwa ba wannan ma ai sun isa...." Kukanta ne ya tsaya cak tunawa da tayi da yadda ya fita a d'akin,yanayinsa ya bata tsoro ita da basu tab'a samun sab'ani ba da shi,shi ne yanzun zata jawo ya fara tsanarta,kalmar *TSANA* data fad'o mata yasa tayi saurin mik'ewa tana kaiwa da kawowa,a fili ta shiga magana da kanta tana fad'in "Wayyoo Allah! ya zanyi da shi,shi kenan na jawowa kaina fushin Allah zai sauka a kaina.... Idonta ta fiddo waje tana dafe kanta da sauri ta shiga cire kayan jikinta,cikin closet enta ta bud'e side en nightys enta,wani maroon colour silky ta fiddo wanda da ganin alama ba a tab'a amfani da suba sai data gama waresu tsaf ta kuma gama k'are musu kallo 3in1 ne kayan d'aya singlet ne,sai doguwa wadda zata kai har k'asa da mad'auri a gefen k'ugunta,d'ayan kuma rigane da wando do go,duka singlet en tsayinsa bare wuce saman knees entaba ta gabansa daga sama kuma wani ado aka masa da net,sawa tayi sannan ta tsaya kallon kanta ta cikin mirror dake gabanta,kayan yayi shara² sosai ta gaba kallon yadda suka bi jikinta take ta cikin kayan ana iya ganin hatta da nipples enta,gashinta ta tattara gefe ta masa tufka d'aya sannan ta kwantar dashi ta gefen necklace enta inda ya sauka har kan chest enta,sosai hakan da tayi ya mata kyau,idanta ta kalla yadda suka yi ja saboda kukan da tayi a hankali ta nufi toilet,sai da ta wanke fuskarta ta kuma sake kama ruwa da ruwan d'umi sannan ta fito,jingina tayi jikin k'ofan kanta a sama tana tunanin mafita,kanta tayi saurin d'agowa tunawa da abunda UMMI ta bata kafin ta fito da ita,da sauri ta nufi hand bag enta daya ajiye mata jikin abunda take sak'alesu,sai data d'auko abun a leda bak'i sannan hankalinta ya kwanta,wani ajiyar zuciya ta saki sannan a fili ta furta "Sam na manta ma da wannan abun wallahi da duk haka bai faru tsakaninmu ba..." Tunowa tayi lokacin da ummi ke mik'o mata abun bayan ta gama bata na gyaran jikin,tambayan da tayiwa UMMI da amsar data bata ta sake tunawa _UMMI mene wannan..?_ _Karb'i ki ajiye zai miki amfani nan gaba.._ _To amma UMMI mene amfaninsa shi...?" _Wannan da kike gani y'ay'an angurya ne...yana da amfani sosai ga macen data haihu,yana taimaka mata musamman gurin hanawa ta sake samun ciki da wuri,kinga ba sai kinyi planning ba ko dan gudun samun matsala da mai gidan naki,idan hair bai yadda ba za kuyi ta samun sab'ani,wannan zai taimaka miki har sai kin samu kin yaye wanda kike shayarwa..._ Karb'a tayi tasa a jakanta sannan ta mata godiya.. 'Dan murmushi tayi da sauri ta d'ibo a hannunta tana dubawa,maidawa tayi da sauri kuma tayi parlour,ruwa ta d'auko da cup sannan ta dawo d'akin,a nan tasha sannan ta maida ragowar muhallinsu tana murmusawa,fuskarta ta gyara tare da murza powder kad'an ta shafa lip stick enta da yake matuk'ar k'auna. Bakin bed enta ta koma ta d'auka d'ayan rigan wadda take doguwa har k'asa,ta d'ora a saman ta jikinta sannan ta kama mad'aurin ta d'aure,addu'a ta tofe yaranta da shi sannan ta fice tana nufan bed room ensa duk da irin yadda zuciyanta keta tsinkewa. Cike da fargabar abunda zata tarar ta tura k'ofan da sallama a bakinta cikin sanyi,can k'asan mak'oshinsa ya amsa mata ba tare da ya kalli inda takeba,hakan da yayi yasa ta sha jinin jikinta,sai dai kuma tunawa da ita ta janyo komai yasa ta aro jarumta ta lik'a ta kuma ci gaba da shiga cikin d'akin,shirin kwanciya yake hakan yasa ta isa gabansa da niyyan taimaka masa,sai dai ko data k'arasa tana k'ok'arin taimaka masan matsawa yayi a gurin,cikin sanyin jiki dan kam ya gama kashe mata gab'ob'i ta furta "Kawo na k'arasa maka...." A tak'aice ya bata amsa da "Barshi ban buk'ata..." Sosai ta tsorata da abunda ya fad'a bata kuma ce masa komaiba ta nufi bakin bed ensa tana shirin zama,muryarsa da tambayan da ya watso mata suka sa ta kasa k'arasa abunda tayi niyya "Me za kiyi a nan...?" 'Dan juyawa tayi tana kallonsa,shi enma itan yake kallo da fuskarsa da take d'aure tam kamar an aiko masa da sak'on mutuwa "YAYA kwanciya zanyifa..." Ta bashi amsa kamar za tayi kuka "Su kuma yaran nawa wa kika bawa ajiya...?" 'Dan kallonsa tayi cikin rashin damuwa ta shiga ware mad'aurin rigar had'e da zareta a jikinta tana kwanciya saman bed en nasa ta furta "Ai sunyi bacci..." Kansa ya kad'a yana fad'in "Na san sunyi bacci ai...Tambayar dana miki itace...Wa kika bama ajiyarsu...?" "Kamar yaya...? naga dai ko can gidan UMMI ma ba tarefa muke kwana dasuba..." Fuska ya dad'a tamkewa cikin fushi ya shiga mata fad'a "Saboda kinga ina had'a shimfid'a dake shi yasa kika raina ni ko...Wato ga sakarai shi ne zaki dube ni kina gayamin ba tare kike kwanciya da suba.... Barin fad'a miki kuma ki bud'e kunne sosai kiji ni daga yau in sake miki magana ki bani irin wannan amsan na rainin wayo.....shi kenan dan kinga na miki ciki kin haihu sai ki ce zaki min abunda kika ga dama....wallahi idan baki maida hankalinki a jikinki ba zan daka ki,ki shiga hankalinki kinji dai na fad'a miki,kuma yanzun ba sai anjima ba kizo ki ficemin a d'aki...Ko an fad'a miki ni jarababbene da zaki kwaso jiki ki biyo bayan kin nunamin iyakata.... Wannan ya zama na k'arshe kada ki kuskura ki sake barin min yara su kad'ai da sunan su kad'ai zasu kwana,duk ranar da kika sake kuskuren yin haka Allah sai nayi mugun sab'a miki..." Yadda ya bad'e idanunsa da toka yana ta zuba fad'a yasa ta fashewa da kuka mai cin rai,cikin k'unk'unin kuka take furta "Dama nasan haka sai ya faru wata rana,duk wanda zai maka alk'awarin soyayya ba zai tab'a iya cikawa ba,tun dana taso na rasa wanda zai soni a rayuwata,na rayu da mahaifina wanda ya zame min uwa da uba....Duk duniya shi kad'ai ya soni....meye laifina a rayuwa da kowane lokaci idan na samu nutsuwa sai wani abu ya gilma tare da disashe farin cikina...? Ban san me nayiba a rayuwa da ko wane bayan zamani saina shiga k'unci,bayan duk irin rayuwar da nayi a baya tun daga gidanmu bare sa a tausaya minba...Haka na koma tamkar mabaraciya a lokacin da nake neman rufin asiri daga mahalicci wanda ya janyo har wasu suke zagina a matsayina na *Y'AR GARUWA* wacce bata da wani sauran gata,a lokacin kowa kallon y'ar iska yakemin wadda ta gudu daga hannun iyayenta,ba dan Allah yaji k'aina ba ya had'a ni da matar da ta rik'e ni a matsayin y'a ba,da haka rayuwata zata ci gaba da tarwatsewa kenan,shin yanzun kuma mene ne laifina dan nayi wannan maganar....?" Ta k'arashe tana sake rushewa da matsanancin kuka,wani kallo ya shiga watso mata cikin k'unar rai ya furta "Kada ki kuskura ki zageni ko mahaifiyata,dan naga rashin mutunci kike ji dashi,idan har kika kuskure kika zageta zan nuna miki iyakarki..." Kukanta ne ya tsaya cak jin maganar da yake,da sauri ta goge fuskarta tana fad'in "Ni ban isa na zagetaba,hasalima idan dan kana tunanin ina magana ne akan itace sanadin daya sa nayi wannan rayuwar a baya to ka daina,na sani tun ran gini ran zane,k'addarata ce kuma dole sai haka ya faru....Saboda haka kayi hak'uri ni ban isa zagin mahaifiyar kaba bare kuma kai..Ina rok'on Allah da kada ya bani ikon aikata haka...Kayi hak'uri ka yafemin nasan na b'ata maka rai,amma dan Allah ka yafemin..." Bai sake kulataba dan yasan idan yaci gaba da magana to tabbas daren yau bazaiwa kowannensu dad'iba,saman bed ya zauna yayi addu'o'insa sannan ya kashe light en d'akin yayi kwanciyarsa. Nan tsaye inda ya barta take har lokacin wasu siraran hawaye masu d'umi suka sake zubo mata,cikin sanyinta ta nufi hanyan fita tana kuma mamakin abunda ya faru,Wanda ko cikin bacci aka fad'a mata haka zai faru tsakaninsu zata k'aryata,har ta fice bai ko sake kallon inda take ba. Saman bed enta ta zauna dafa'an ta shiga rera kuka mai ban tsoro da tausayi,cike da tashin hankali take kuka tana k'arawa,dan kanta kuma ta rarrashi zuciyarta sannan ta d'auko LITTLE tasa ta a gabanta sannan mazan dake kusa da LITTLE hannunta ta d'ora samansu tana sake had'asu da jikinta,da k'yar bacci ya d'auketa sai ajiyan zuciya take saukewa da k'arfi. B'angaren BB ma hakan ce ta kasance,lokacin data fita a d'akin yana kallonta tana goge fuskarta akai²,maganganunta ne suka shiga yi masa yawo cikin kansa,tausayi had'e da soyayyarta lokaci d'aya suka kawo masa ziyara wanda suka sa sam sai yaga baiga laifintaba cikin abunda ya faru kuma gaskiya ta fad'a ba tare suke bacciba dan UMMI ma ta fad'a masa,kukanta ne ya shiga dawo masa a cikin kunnensa,mik'ewa yayi ya shiga safa da marwa cikin d'akin har dare yayi nisa idanunsa biyu ya gagara bacci,nan zuciyoyinsa suka shiga kawo masa shawarwari daban-daban sunata fafatawa akan yaje ya rarrasheta,d'aya kuma na fad'in hakan da yayi mata shi ne zaisa ta gane kuskurenta ko nan gaba,dan taga yana tsananin sonta ne yasa zata fara masa iskanci,hakan da yayi mata ko zaisa ta gane nan gaba kuma bazata sakeba,yayin da d'ayan gefen na zuciyarsa ke sanar masa da,idan ya duba halayyarta kuma da tsayin zamansu ai bata tab'a masa laifi makamancin haka na,tabbas idan yayi mata haka bai mata adalciba,kuma ina al'k'awarin daya mata na killace soyayyarta har k'arshen numfashinsa,zuciyarsa ce tayi wani irin bugu tunawa da alk'awarin,kasancrwarsa mutum mai girmama alk'awari,nan ya shiga tunani iri-iri akan yaje ya rarrasheta ko a'a,kwanciya ya sake yi lokacin da ya amshi shawarar kangararriyar zuciyar tasa. Sai daifa a banza yadda yaga rana haka yaga daren ranar,sam bacci ya gagari idanunsa,ba shi ya samu bacciba sai wajejen k'arfe biyu,wanda ya haddasa masa yin sallah a makare. Ko bayan daya idar bacci ne ya sake d'aukansa dan dama ba wani bacci yayiba sosai a daren. Da asuba ta tashi tayi sallah kuma har lokacin yaran basu farka ba,baccinsu suke hankali kwance,sanin bata da mataimaki yasa bata yi tunanin komawa ta kwanta ba,fita tayi ta fara y'an aikace aikacenta,sai data gyara ko ina na cikin gidan sannan ta shiga kitchen da tunanin abunda ya kamata ta musu na break fast,markad'ad'd'iyar gyada ta d'iba ta dama dan kam kunun gyad'a kawai taji tana sha'awar sha a safiyar kuma dama ganin tana so yasa UMMI ta had'ota da gyad'ar. Zuciyarta duk babu dad'i haka take aikin saboda abunda ya had'asu jiya ya tsaya mata a rai,sai data gama ta shirya komai a dinning,ta dawo zata wuce bed room da niyyan dubawa ko sun tashi,dan tun d'azun data fito tana aikin tana dubawa amma tsill saita samu sunata bacci abunsu. Doorbells taji na k'ara da sauri ta nufi gurin dan dubawa a ranta kuma tana mamakin waye da wannan safiyar..? Bata tambayaba sai data lek'a a hankali kuma ta bud'e k'ofar ganin wata y'ar dattijuwa tsaye yasa ta saki fuskarta tana fad'in "Sannu da zuwa..." Amsawa matar tayi da y'an kayanta cikin wata y'ar jaka tabi bayan KHUBRA,bayan sun gaisa cikin sakin fuska,matar ta shaida mata UMMI ce ta turota yanzun driver'nta ya kawota,kuma itace wacce zata kula da yaran,murna sosai KHUBRA tayi dan dama zuciyarta duk a dame take da tunanin yadda za ta dunga ma yaran wanka ta kuma shirya su.Godiya ta mata sannan ta d'auki kayan matar mai suna SABUWA tayi ciki ita kuma tana biye da ita har bed room enta inda yaran ke kwance,nan ta zauna tana kalle-kalle na yadda tun daga get en gidan ya zama abun kallo ashe tace bata ga komaiba,wanka KHUBRA ta shiga bayan ta fito ta shirya cikin riga da sket na wani atamfa daya matuk'ar yi mata kyau,ta kafa d'aurin d'ankwalinta kamar gwagwgwaro,sannan ta fad'awa SABUWA tana zuwa ga yaran nan ko da zasu tashi bata nan,nan ta nuna mata komai a sauk'ak'e sannan ta fice. Ficewa tayi fuskarta tasha kwalliya sai dai kallo d'aya zaka mata ka gano bata tare da nutsuwarta haka nan dai ta isa d'akin nasa,kwance ta tarar da shi har lokacin yayi hugging pillow so tight,duk sai taji wani iri da bata aikata abunda tayi ba da tuni itace haka kwance jikinsa kamar ko wane lokaci na can baya,rashin jin dad'in ne ya rinjayi zuciyarta wani missing ensa ya taso mata daga can k'asan zuciyarta,k'afafunta taja cikin sanyi ta isa kusa dashi ta zauna,hannunta ta d'ora saman kansa tana shafawa murya k'asa-k'asa saboda kuka dake neman kufce mata ta furka "Ka gafarce ni mijina na san ni mai lefi ce a gareka,amma banyi dan na b'ata makaba,sai bayan da nayi ni kaina abun ya dameni...Dan Allah kace ka yafe min ko zan samu nutsuwa da sukuni.In Allah ya yarda haka bazai sake faruwa ba da izinin Allah..." Kamar wacce take magana da mutumin dake ido biyu taketa surutanta,hawaye na sakkowa kan fuskarta har ta k'araci maganganunta tayi shiru,mik'ewa tayi da miyyar komawa gurin SABUWA,taji an rik'o hannunta,da sauri ta juya ta kalleshi ga mamakinta idonsa har lokacin a kulle suke,mamaki ne ya cikata da ganin hakan,k'ok'arin zame hannunta taci gaba dayi,cikin siririyar murya ya furta "Ina zaki jene...kike k'ok'arin k'wacewa..?" Sake kallonsa tayi taga da gaske shi yayi magnar ko kuwa.? sai dai wannan karon data kalleshi sai taga ya bud'e idanunsa kuma ita yake kallo,kanta ta sauke k'asa ba tare da tayi maganaba,abunda KHUBRA bata saniba tun daga shigowarta d'akin BB yana ganinta ta tsakanin lashes en idonsa,kawai dai yayi mata fakare ne ta yadda za tayi tsammanin bacci yake,saboda haka duk maganganunta babu wanda bai jiba kuma sosai yaji ya samu nutsuwa a lokacin. Dawo da ita yayi ta zauna sannan ya mirgina jikinta,kansa ya d'ora kan k'irjinta hannayensa zagaye da waist enta ya shiga sauke wani wahalallen ajiyan zuciya,a b'angarenta kam ko iya haka kad'ai yabar ta tabbas ya gama mata komai dan kam ji tayi kamar an mata gafara,da sauri ta rungume kansa tana sakin ajiyan zuciya,yanayinsu kad'ai ya isa ya bayyanar da yadda sukai missing junansu,kansa ya d'ago yana kallonta da sauri ya dad'a kusanta bakinsa da nata,bai jira jin komai ba ko shawara da kowaba ya shiga aika mata da zallar k'aunarsa cake sawa ta manta ita wace,suna yi suna exchanging word's da suke nuna tsantsar yadda sukayi kewar junansu. Cikin lokaci k'ank'ani suka manta da duk wani abu daya faru dasu,sun yi nisa cikin wata duniyar ta daban da babu wanda suke tunawa face kawunansu,sun farantawa junansu inda suka manta da duk wani abu daya had'asu a wancan daren. Haka rayuwarsu ta ci gaba da tafiya a yayinda kowanne ke kaffa-kaffa da gujewa b'atawa d'an uwansa,basu da aikin daya wuce farantawa junansu da kyautatama junansu,inda yaransu kuma suka ci gaba da samun kulawa k'arkashin jagorancin BABA SABUWA da tun zuwanta gidan yaran suka koma gurinta,komai ita ke musu idan ka gansu gurin KHUBRA to abincinsu suke nema wanda wani lokacin idan suka tashi tsiya lokaci guda zasusa mata kuka,ba dama ta fara karb'an d'aya sai sauran susa mata rigima,ita kuma abunda ke d'aga mata hankali kenan sai kaga ta fashe da kuka,idan an tambayeta sai tace _"Ita bata san ya za tayi musu ba,shi kenan babu damar su kyaleta ta huta.."_ Haka za tayi ta fama,har sai BB ya rarrasheta tukun zata hak'ura tayi shiru,wani lokacin ko shima da kansa zai sata gaba yana tsokana musamman idan ta fara kumbura fuska tana k'unk'uni shima haka zai kwanta kan cinyanta cike da shag'wab'a yana fad'in "MOMMAH....saura PAPA shima yana buk'atar ayi feeding nasa..." Duk lokacin daya mata haka sakin baki take tayi ta kuka tana fad'in "Shi kenan kuma na shiga tara..tunda so kuke ku na mutu sai ku kasheni ai sai ku rabani hud'u kowa ya huta.." Shi ko nan zai sata gaba yana dariya,idan yaga ta tsananta kukan ne zai dena ya kuma koma rarrashinta...Ranar da kyar zai samu tayi shiru har ta sakko daga Fushin da take yi............ *EIGHT YEAR'S LEAP.....* Kwance take saman bed da waya a hannunta tana latsawa,da ganin alamu kuma chart take,sai dai na d'an sake matsawa kusa dan ganin abunda take yi,nan ko na ganota tana shawagi cikin group en nasu da ba wani yawa gare suba,dan duka bana jin zasu haura su goma.. Hira suke cike da k'aunar kasancewa tare a haka har k'anshen rayuwa. Shigowar BB yasa ta ajiye wayan a gefenta tana murmusawa.Cike da so da k'auna BB ya kalli KHUBRA data zama babbar hajiya yana kwanciya saman jikinta,cikin wani voice dake kashe mata duka gab'ob'in jikinta ya sake kallonta,ido d'aya ya kashe mata yana fad'in "JODI yaushe zaki sake bani new baby ne...? ina son sake ganinki da babyna kwance a nan...?" Ido ta fiddo tana rufe bakinta da hannu ta furta "Haba MY JAAN....Yanzun har fatan na sake haihuwa kakemin...? yara biyarfa nake da su..Inama laifin kace na barshi haka ai nayi k'ok'arima hakan..." Y'ar dariya yayi yana fad'in "Haba mana dan kin bani biyar shi ne kike rakin kinyi k'ok'ari...?" "Ehh! mana kaima kuma ai kasan nayin indai k'ok'ari ne,kallafa CWEETY har yanzun a uku take,dama dama ma ASHNA da muke kai d'aya,amma itama ai ta rigani haihuwan fari,kuma kana dai ganin CWEETY ko shirin sakewa bata da.Daga maza biyu mace d'aya face ya is a haka..tabbb! ni dai kayi hak'uri hakanma Allah ya raya mana su cikin aminci..." "To ameen...Amma dai da kin daure kin k'aramin ko dozin biyu ne..." Yadda tayi da fuska yasa shi kwashewa da dariya,pillow ta d'auka tana dukansa shima ya d'auka yana ramawa,zuwa can kuma suka zube suna maida numfashi game da dariyar farin cikin yadda rayuwarsu ta kasance... Tsagaitawa tayi da tata dariyar tana shafa fuskarsa,da sauri ya kalleta yana d'aga mata gida alaman tambaya,a hankali ta motsa bakinta cikin coolness "Kawai YAYANAH idan na kalleka da yaranmu sai na tuna rayuwata ta baya ne lokacin da nake matsayin *Y'AR GARUWA...* sam ban tab'a kawowa rayuwata zata zamo yadda nake a yanzun ba...Alhamdulillah! komai yayi farko da sannu k'arshensa zaizo...yau ni ce kwance jikin mijina abun alfaharina,baya ga yarana dake kewaye da ni a kowane lokaci...Tabbas Allah shi ne abun godiya..Allah na gode maka bisa ni'imomin da kaimin..." Siraran hawayenta dake mak'ale a idanunta suka sakko. 'Dan murmushi yayi yana dad'a mannata da jikinsa,cikin kunnenta ya shiga fad'a mata magan-ganun da zasu sata ta manta da damuwar da ke neman kunno mata kai,sai da yaga ta ware sosai sannan ya furta "Tohh! MR'S KHALEED SAFWAN yanzun komai ya wuce ai kuma maganar kin tab'a yin wani wahala da har ya kai ki zama matsayin *Y'AR GARUWA* ina so ya wuce,coz ban son wata rana wani yaji bare har ya gorantama yaranmu.....Tun da kin jima da barin wannan layin,kuma ko a yanzun aka kalleki babu wanda zai yarda kin yi irin wannan rayuwar,saboda kina da abubuwan da zasu gogema mutum tunanin haka,kina da ilimi bayaga nasarori da kika samu a rayuwa,yanzun kina a matsayin mata ga MR KHALEED SAFWAN,after all these gashi har kin haifamin sanyin idaniyata kuma abun k'aunata,so kada ki damu ako da yaushe zamu ci gaba da kasancewa tare kamar farkon auren mu...So yanzu komai zai koma FREE..... *LOVE FREE...!* *KISS FREE...!!* *LIVE FREE...!!!"* Dariya dukansu suka yi yana dad'a rungumeta a jikinsa had'e da sakar mata fake a Cheek's enta,da gudu yaransu suka shigo maza uku mata biyu suna fad'in *"PAPA nd MOMMA.....APPY WEEDING ANNIVASERY...."* Da mamaki iyayen suka kallesu coz basu san inda suka jiba,LITTLE ce ta kalli iyayen nasu tana fad'in "PAPA..... UNCLE ne ya fad'a mana jiya da muka je gidan Granny's..." Cike da nishad'i BB ya bud'e musu hannu inda MOMMA'NSU ke kwance cikin jikinsa wanda ganinsu baisa ta tashiba,da gudu ko suka k'arasa suna dariya dukansu ya rungume yana jin sonsu har cikin b'argonsa.... "To yanzun kowa ya yazo fad'amin abunda yake da buk'ata a yau ni kuma nayi muku alk'awarin bawa kowa abunda yake so..." Kallonsa HAJIYA KHUBRA tayi tana murmushi,shi d'inma ita yake kallo kuma yana maganar,da sauri LITTLE dake da shekara takwas a lokacin ta furta "PAPA mu dai da kid sis a kaimu saudiyya muga d'akin Allah...irin na photon nan..." Ido KHUBRA ta dad'a bud'ewa tana kallonsu da mamaki coz batayi tsammanin jin hakaba daga bakinsu,sai dai amsar *ALHAJI KHALEED* tasa ta binsu da kallo dan ko amsa musu yayi da fad'in "An gama...ku shirya in sha Allah idan kuka yi hutu a skul zamuje Umra next month...." Ihu suka d'auka duka yaran suka sake rungume iyayen nasu suna fad'in *"WE ALL LUV AND PROUD WITH U PAPA ND MOMMAH..........!"* ~K'ARSHE.....~ *ALHAMDULILLAH...!* *ALHAMDULILLAH...!!* *ALHAMDULILLAH...!!!* _A nan na kawo k'arshen wannan littafi nawa na *Y'AR GARUWA..* Ina mai mik'a d'umbin godiyata ga Allah (S.W.T) daya bani iko,dama da kuma lafiyar dana kawo k'arshen wannan labari nawa,inda nayi kuskure ubangiji ya yafemin ni daku,inda kuma nayi dai² Ubangiji ya had'amu a ladan..._ _Sannan ina mai mik'a godiya ga masoyana,y'an uwana,dama magoya bayana,da sukayi jimirin ci gaba da bina cikin saurarena akoda yaushe,inda har ga shi na samu na kawo k'arshen wannan labari,Allah yasa jama'a suyi amfani da darussan dake cikin wannan labari,ina godiya sosai tare da fatan alkhairi a gareku masoya....Sai mun sake had'uwa nan gaba idan Allah ya nufa...Fasubhanakallahumma wabii-hamdika nash-hadu an-laa-ilaha illa-antaa nastagfiruka wana tubu ilaiik........._ _TAMMAT BII HAMDILLAH...!_ _FOR CORRECTION'S/COMMENT'S JUST CONTACT ME @MY WHATSAPP ACCOUNT +2348125527472._ *UR'S AND ONLY....* *_®єαl $mααhєr._* 😉