🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 🫶 *AZAL!* 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *SAJIDA NIJAR* *PAID BOOK* _Bismillahir rahamanir-rahim._ *1* *wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nigar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍* *TALLAH, TALLAH, TALKAH* _*TOH TO TO!*_ 🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_ _Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_ Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake _Amarya_Uwar gida_ _Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_ _Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_ INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼 🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI* *🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU* _KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_ _SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_ 💁🏽‍♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻* 💁🏽‍♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI… _MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_ *ADRESSE 94536935 94.53.69.35* *Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER* MASU BUKATAR SHIGA GROUP INMU DAN GANI DA IDO👀 AKACE YAKORI JI👂🏼 DANNA WANAN LINK DIN ZAI SADAMU DAKU🤝 https://chat.whatsapp.com/INwtTlr1yFQ5B0AQa2DM6d KARKU SAKE ABAKU LABARI🥳 Litattafan marubuciyar Duk karyar kada Yar mahaukaciya Bak'a ce Bani da zabi Daga tafia daukar soja Neman na kaina Kutkale Mage Bani da zabi Idan ka raina inda kake Umughuluk itifal Duk nisan jifa Wata kokowar Ni zan ladabi Dakika biyar Da ciwo a zuciyata Aure yakin mata Alkalamin Kadarata Dutse Daga tafiya daukar soja Makauniyace ND now *AZAL* Kwata kwata ya manta cewa wayarsa ce jone a jikin lasifikar motar dake tafiya da su daga sabon Gari zuwa Anguwar Jeune cadre, hakan ya sa ya gyara zamansa daga gaban motar dake dauke da su, su uku yana sake buga numbar yarinyar nan ama cikin ikon Allah sam ba'a daga ba. Da mamaki ya sake dubawa, eh lalle numbar ce, tunda aka turo masa numbar da hoton mai numbar bai cenza komai Da dan dabara ya kalli wanda ke hakimce a bayan motar yana kallon hanyar nan baya ko kiftawa hannunsa sama wajen girarsa a hankali yana shafa wajen yana tunanin abinda ke cikin ransa A kira na kusan tara aka daga wayar, sai dai babu amsar da aka bada da ta wuce shiru da shuuuuuuuuuuu tamkar karar fanka "Asalamu alaiki, dan Allah ina magana da RAUDA ne?" Ya fada yana sauraro da tabacin zai ji amsa daga ɓangaren wace aka kira da RAUDA domin a irin labarin da aka bashi na ita din wacece ya san ko Muryar yaro karami ta ji in dai namiji ne zata saurara Shiru ya dauki wayar da motar baki daya Sai da ya ja numfashi ya sake furta" Wai ko ba'a jin muryana daga wayar ne?" Daga ɓangaren wace aka kira da RAUDA ta ja wani arnen tsaki sannan ta datse kiran Tsakin da ya ratsa baki daya motar har cikin kwakwaluwar mutumen dake bayan motar nan zaune A hankali ya lumshe idannuwansa sannan ya bude a kan wanda ke gaba zaune daidai lokacin da ya zarro ido ya ciro wayar a rikice ya zuba dubansa yana duban wayar tamkar wanda ke son karantar wani abu a jikin wayar Muryarsa a yannayin dimauta ya shiga magana tamkar ba abokinsa ne ke zaune a motar Ba ya ce" YUSEF, Walahi ban san bata da mut......" Shiru ya yi da maganar da yake yi sakamakon gannin motar na tsayawa dan a bude masu get YUSEF din ya bude motar ya fice bai ce da shi ci kanka ba A kafarsa ya shige baban get din gidan nasa , du irin tsayin tafiyar dake gabansa cikin tafiya ta nutsuwa da kwonciyar hankali A birkice wanda ke cikin motar ya dafe gaban goshinsa lokaci daya ya shiga kiran numbar wace ta bashi numbar Nafisa na dauka ya shiga masifa yana fadin" Yar gidan uban waye kika bani numbarta? Dama bata da mutunci ko bata san abinda ake iya kiranta dominsa bane? A kan mi zaki bani numbar baki min bayanin komai ba?" Nafisa ta yi dan firgigit sakamakon barcin da ya fara fizgarta na bakin magariba dan ta gaji ainun , daga wajen biki take har juwa ke kwasarta dan gajiyar rawar da suka tika tana wara idannuwanta ta ce" Ban gane ba da ka kireta me ta ce da kai?" Rai bace ya ce" da na yi kiranta tsaki ta yi ta katse wayarta, ke kin san waye za'a kawowa ita?" Nafisa ta dantse lebe cike da takaici ta ce" Ba yar uban kowa bace , dama a yadda na ga alamun fadin ranta sai da nace da kai oga du yan matan nan ita ta maka? Kace eh, menene kake nema a wajenta wanda babu a wajen sauran? Ama ka yi hakuri zan tardata sai na mata rashin mutunci, Duda ba ni ta ba numbarta ba , Ni ko magana bata taɓa hadani da ita ba dan na tsani ire irin yan matan nan masu shegen dagin kan tsiya!" Takaici ya saka shi kashe kiran ya bude motar ya fice shima ya shiga a kafar yana takawa da sauri dan burinsa ya je ya bashi hakuri , dan shi ya san shirunsa ba alkhairi bane A lokacin da ya karasa bangarensa da kyar ya kama madubin kofar ya bude ya shiga , a nan ya sake yarda cewa mutumen da ya tsane su na wajen, dan haka sai ya kama kansa bayan ya yi salama ya nufi kujerar zaman mutun daya ya zauna yana sake kama kansa Tunda ya shigo RISLAN ya yi shiru da bayanin da yake yi sannan ya daure fuska yana jin kirjinsa har zafi yake yi saboda yawon da ɗan uwansa ke yi da ISHAK , yawo na shashanci, yawo na watsar da kai da watsar da adini Murmushi kadan YUSEF ya yi yana dauke dubansa daga kan RISLAN ya dan dubi Ishak ya ga ya gyara zama bashi da niyar tashi bayan ya tarda magana suke yi wace ta shafi family isu Dan gyaran murya ya yi a hankali ya ce" ishak shiga ciki mana " Ishak din ya mike yana jin zafin RISLAN har kasan zuciyarsa, domin a duniya wannan mutun yana matukar saka masu ido a shige da ficensu da YUSEF, ama shi jiransa yake yi wata rana ya shiga huruminsa WALAHI sai ya nuna masa bashi da wayo! Dan ya nuna masa dan duniya ne shi Ciki ya shige yana hura hanci, Sai da ya shige RISLAN ya iya sauke ajiyar zuciya ya sake fuskantar YUSEF A tausashe ya ce" ya dace ka san me kake ciki zuwa yanzu, ya dace ka yiwa kanka wa'azi ka kuma gane a kulun shekarunka karuwa suke yi ba ragewa ba, ka sada kanka ka yafe wasu abubuwan ka kuma kyale wasu ka rayu da su a haka, ka je ka ga HAJIA ana ruwan saman nan na jiya ta fadi ta samu karaya kuma an kirayeka an sanar maka, HAJIA fa mahaifiyar mai martaba ce YUSEF" Murmushin nan nasa wanda yake kama da ashariya ya sakar masa kafin ya dauke dubansa a Nutse ya ce" To " RISLAN ya zuba masa ido da duba irin na tsoron yannayinsa Hannayensa ya hade yana dubansa ya ce" Yaya zaka ce to bayan na san ba yi zaka yi ba? Dan Allah na roke ka ka je....." "Kar ka saki ka rokeni kan abinda bai zame mini wajibi ba!, na goge zumuncina da ita, ubana ta haifa ba Ni ba shine dolenta, maganar na bar abinda nake yi nace maka to zan bari, me yasa kake so sai ka saka na daga maka murya ne?" Ya fada a kausashe, ama a hankali dan ko me yake yi tsakaninsa da ɗan uwansa bai taba yarda wani ya ji ba RISLAN ya rintse idannuwansa da suka cika taf da kwallah, wannan wani irin Fitina ne ke yawo a jinnin ahalinsu, sai kace ba jinnin sarauta ba? Daga mashaya sai mazinata, sai masu halaya irin na bera? Ya Allah ka dubu lamarin wannan ahali A hankali ya ce" Ka tabbata zaka je dan uwana?" Shiru ya yi da farko, sai kuma ya sakar masa murmushi a hankali ya gyada masa kai ya ce" Zan je bi izinillah" "Ka san me Abanmu ke buri? Burinsa ya ga ka yi aure kaima, ka san burinsa ya ga kaima ka kawo matar da kake so ka yi aure Dan uwana" RISLAN ya fada a tausashe yana sake zuba masa ido dan gannin reaction dinsa Mikewa YUSEF ya yi a Nutse ya bale rigar dake jikinsa ya cireta ya ajiye nan saman kujerar falon ya zamto abinda ya rage a jikinsa farar singileti ce cikin nutsuwa ya juya ya nufi wajen frij din falon ya bude ya ciro galan din ruwa mai sanyi ya juyo ya dawo falon ya bude yana mika masa Amsa RISLAN ya yi yana furta" Thank you" YUSEF ya zauna yana janyo computersa ya bude ya yi connecting da wifi din gidan sannan ya ajiye ya juyo ya zubawa RISLAN ido kamar yadda shima yake kallonsa Murmushi ya yi a Nutse ya ce" Ni fa ba mata bane bana so, Idan na ki mata waye zai bani abin sakin mara?, Usatz soyayya da mace daya ne nake yiwa lakabi da *AZAL*!, ba zan taba yarda ganganci ya jani wannan ba, aure kuma ka cewa babanka kar ya damu idan na shiryawa hakan zan kawo mashi hudu ya kula!" Tunda ya fara bayanin a tausashe ne, harufan a bayyane ne, sai dai yannayin maganar wani iri ne tamkar wanda baya son fitar da amon muryarsa , ko dan abokinsa na ciki? Wanda yake yiwa boyon sirin dake tsakaninsa da ɗan uwansa ne? Maganar dai gatanan tamkar wanda ya maku haka dai , sama sama dai kuma kasa kasa dai, maganar kamar wanda yake so daga shi sai RISLAN zasu ji ta "Soyayyar ce *AZAL?* soyayya itace abar da ta fi komai dadi a duniya, wanda baya so bai morewa rayuwa ba, kai da ba dan so ba ai da duniyar nan ta tashi, soyayya farin ciki ce, kwonciyar hankali ce, nutsuwa ce, kar ka yi mamakin ka wayi gari ka samu kanka a cikin so YUSEF " RISLAN ya fada a tausashe yana kallon Yusuf Dan murmushi ya yi ya masa shiru, bai dauki computer ba da da irin tarin aikin dake gabansa, dan shi din yana da halaya mabanbanta ne, koda Akoy hali taurare Akoy sansanyan hali a tare da shi, YUSEF yana da daraja mutane da yannayi irin nasa Gannin yanzu firar ta zama ta shi daya a dole ya mike ya yiwa YUSEF Salama sannan ya yi tafiyarsa yana ji inama zai iya da ya shiga ya fitar da wancen dan dabar dake ciki dan ba zai so ya fitar da shi ba a gabanan kuma, yana addu'a a kulun Allah ya shiga tsakanin dan uwansa da bata garin nan, su din da kansu yana binsu da Adu'ar shiriya Bayan tafiyar RISLAN da kamar minti goma sha biyar ishak ya fito daga ciki ya karaso ya zauna dan nesa da YUSEF kadan a tausashe ya ce" Dan Allah ka yi hakuri da wannan banzar cikar da ta yi maka tsaki dazun a mota"" YUSEF ya dan dakatar da dogon rubutun da yake yi dan yana nema ya bada shi sanadiyar maganar da ya fada wace bata da wani tsari Ishak ya ci gaba da fadin" ban san marar rabo bace sai da ta aikata aikin jahilai da wa'inda basu da rabo ba, ama Ni na yiwa kaina alkawarin sai na masheta doki ta yadda kowani kare zai hau tunda har ta kasa amsar mai daraja irinka" "Ka daina magana sama sama mana ina typing din abu muhimi ne" YUSEF ya fada tamkar bai ji magangannun da Ishak ke fada ba Shiru Ishak ya yi, baya so ne ya fita ya bar shi a wannan yanayin ya san ya bata masa, shi yasa ya tsaya dole dan ya bashi hakuri, Sai da YUSEF ya gama rubutunsa sannan ya rufe computer bayan ya kashe ya dubi Ishak dake zaune gannin ya kashe computer ya ajiye wayar dake hannunsa A Nutse ya ce" Ta san Ni ne da zata raina Ni?, kaine ka raina Ni, ina fatan zai zamo na farko kuma na karshe da zan ga irin wannan rainin ka fahimta?" Ishak ya yi gagawar amsashi har yana bashi hakuri, hakan sai ya daure min kai, domin a tunanina a kuma zatona YUSEF aboki ne wa Ishak, ba yaron gida ba, sai abin ya daure min kai ainun domin shi din kansa ishak shigar jikinsa ta manyan kudade ce, shin menene ya sa yake yiwa YUSEF magana kamar yana yiwa wani wanda ya isa da shi? Isa irin ta iyaye ba ƙawance ba? Ishak bai bar falon ba sai da ya kawowa YUSEF abincinsa dake saman table sannan ya tafi YUSEF ya jima a falon nan bayan ya gama cin abincin sannan ya nufi dakinsa yana jin gajiya tatare da shi da kuma launin bukata irin ta lafiya, wace lafiya ke kawota, ama bacin ran jin tsakin nan ya tsaye masa a kahon zuka Murmushi ya yi kawai yana janyo filonsa fari ya rungume dan ko ba komai ai zai tashi sallar asubahi sannan ga auren Elhaji goben wanda ya tabbata idan bai halarci auren ba yana iya haduwa da surutu mai girman gaske da jajen bai kyauta ba, sai kace auren fari a wani damu mutane da gayata.......... Asalamu alaikum jama'a....mun zo maku da nagartacen ingantaccen maganin Ulcer, magani ne na Hausa jikake wanda Dubai suka gwada suka ji dadinsa, nagartatun tsatatatun itaciyoyin da suka bamu sasake masu anfani ne ake anfani da su, a nan jamhuriyar Nijar a garin Damagaran a farashi mai rahusa dubu biyu yan naija , yan nijer kuwa 1500francs mai bukata ga numbar +227 96897192 , HAJIA RAHAMA 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *AZAL!* 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *SAJIDA NIJAR* *PAID BOOK* _Bismillahir rahamanir-rahim._ *2* *wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nigar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍* *TALLAH, TALLAH, TALKAH* _*TOH TO TO!*_ 🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_ _Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_ Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake _Amarya_Uwar gida_ _Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_ _Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_ INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼 🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI* *🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU* _KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_ _SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_ 💁🏽‍♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻* 💁🏽‍♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI… _MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_ *ADRESSE 94536935 94.53.69.35* *Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER* MASU BUKATAR SHIGA GROUP INMU DAN GANI DA IDO👀 AKACE YAKORI JI👂🏼 DANNA WANAN LINK DIN ZAI SADAMU DAKU🤝 https://chat.whatsapp.com/INwtTlr1yFQ5B0AQa2DM6d KARKU SAKE ABAKU LABARI🥳 Litattafan marubuciyar Duk karyar kada Yar mahaukaciya Bak'a ce Bani da zabi Daga tafia daukar soja Neman na kaina Kutkale Mage Bani da zabi Idan ka raina inda kake Umughuluk itifal Duk nisan jifa Wata kokowar Ni zan ladabi Dakika biyar Da ciwo a zuciyata Aure yakin mata Alkalamin Kadarata Dutse Daga tafiya daukar soja Makauniyace ND now *AZAL* Washe gari karfe hudu da rabi na yama "Rauda, dan Allah ki yi hakuri ki tashi ki yi ja gabar kai abincin nan, kin ga Elhaji baban mutun ne yana da abokai manya da ya dace a darajasu, dan Allah ku je tare kar ki ki zuwa" Amaryar wannan rana ke fada kasa kasa bayan ta rike hannun wata wace ta yi kira da Rauda A hankali Rauda ta lumshe idannuwanta tana jin wani irin nauyi ne kawarta Bara'atu zata dora Mata, sai dai zata yi kokarin ganin ta yin dan ta fidata kunya, domin a tarin kawayen nan nata kamar yadda Bara'atu ne ta fada gagawar da suke na tukwuicin da ake iya basu ne idan sun je kai abincin nan ba na a fitar da ita kunya ba, ita kuma itace babbar kawarta dole zata jajirce ta ga an fidata kunya Tana kokarin mikewa Auntyn Bara'atu wato yayarta salaha ta leko bayan ta bude part din da murmushi kwonce saman fuskarta ta ce" RAUDA, yaushe zaku kai abincin nan ne? Yan matan amaryar nan Akoy jan aji fa, har karfe hudu na neman shigewa baku kaiwa mutane abinci ba?" Rauda ta mike tana mika hannu ta dauki dan madaidaicin mayafinta ta ɗora saman kanta, domin gashinta a bude yake dama ta saka dan karamin ribom ne ta daure shi, ko kitson bikin Babar aminiyarta bata yi ba, hasalima tunda ta samu ta dinka shadar fatiha sai atampar ranar nan daga su bata karra komai ba sanadiyar abinda ke mamaye da rayuwarta Tana mikewar kusan yan matan dake wajen sai faman hoto da vidio suke yi sai da suka yi mata kallon kasa kasa, gatanan dai a yannayin shiga sun dameta sun shanye, sai dai wani irin tsari da Allah ya yiwa halitarta mai zubaben sanyi da jiki luwai luwai yakan zamo abin kallo a wajen du wani mai son kallon abu mai kyau.......... Murmushi ta sakarwa auntyn kawarta ta ce" Yanzu zamu tafi aunty" Sai kuma ta juya wajen Bara'atu ta ce" Ki sanar ma wa'inda zamu je da su Ni Bara na yi gaba" Daga haka ta wuce da yar karamar jakarta a hannunta wace ke dauke da wayarta Takalminta plate ta saka baki mai nutsatsen kyau sannan ta karasa wajen motar da aka saka abincin wajen mazan tun dazu ta bude gaba ta shiga ta zauna ta janyo earpeace dinta ta makala a kunnenta a hankali ta lumshe idannuwanta tana sauraron wakar dake cikin wayar Jim kadan wasu yan matan su uku suka fito, ciki harda wace ta bada numbarta wato Nafisa, dan tunda safe da suka zo ta so tada mata zancen ama Rauda din bata zauna ba, ita kuma ta daukarwa kanta alkawarin sai ta tada mata zancen nan dan ta fada mata me take nufi? Kai ba kowa ba, ba dan kowa ba sai wani isa da takama ta rainin wayo, ta tabata ko waye ke son numbarta ba karamin mutum bane tunda wanda ya tambayarma ba karamin mutum din bane shine zata wani rainawa mutane wayo? Sunna karasowa suka ganta zaune gidan gaba ta wani hade rai , da kyar Nafisa ta yarda ta shiga bayan nan ranta a mugun bace, ta daukarwa kanta alkawarin a zuwa ba ta shiga gaba ba? A dawowa Sai dai baya dan uban ubanta! Da wannan direban gidan su Bara'atu ya ja motar ya nufi gidan su angon da su da niyar kaiwa angwayen abincinsu kamar yadda al'adunmu suke a garinmu, ranar wunin biki yan matan amarya na yiwa angwaye girki gwargwadon iyawarsa su tafi su kai su zuzuba masu idan aka ci aka gama sai a basu tukwuicinsu mai tsoka mai kashi😂 Gaban wani makeken vila suka ja suka tsaya a Anguwar kwaliya dake cikin Damagaran Tunda suka tsaya yan matan nan hankalinsu ya rabu gida biyu, domin ta yadda suka ga jikakun motocin dake parker a kofar gidan nan hankalinsu ya karra tashi, nan fa kan mai fitar da jan baki da madubi daga jaka sai mai fitar da hoda suka shiga sake gyagyarawa, dama kwaliyar yau ta musamman ce, mijin Bara'atu dan kasuwa ne sun san ko ba komai sa jimki kudade da kuma nasu summa abokin rayuwar ko abokin shashancin, lokaci ne Alkali, abinda suka sani a fitowar nan tasu sai sun yi wufff da ɗan wata ko uban wata Ficewa direban ya yi ya je ya bubuga bisa umarnin RAUDA wace kasa kasa sosai ta ce" Baba buga masu kofar Atu tace Akoy kare , idanma daga nan zamu sauke masu mu juya fine" Tana kiransa da baba ne saboda yana dauke da sunnan mahaifinta, sannan mutun ne mai daraja dan Adam, a kulun idan ya dauki Atu sai ya biya ya daukota ya ajiye su a makaranta, tun tana kiyawa har Atun ta kai kararta wajen Mamanta sai ta mata fadan a kan me zata ki shiga a kaisu da kawarta? A dole take shiga har ya zamo kamar yar gidan du inda zasu je tare ake kai su a motar Bugawa ya yi ya fi a irga , gannin ba'a bude ba ya dawo yana fadin" HAJIA Rauda Inaga sai an yi kira ko kawai mu tura mu shiga?" Rauda ta girgiza kai ta ciro karamar wayarta tana masa alamun tana zuwa Numbar mijin Atun ta dannawa kira Wayar na fara ringin ya daga yana fadin" Da girman kujerarki aminiyar aminiyata" Murmushi ta yi , da salon muryarta ta ce" Muna kofa fa aminin aminiyata" Mikewa ya yi da wayar a hannunsa daga cikin mutanen da basu wuce su shida ba, dan kuwa a dole ya tsame daga cikin taron hayaniyar jama'a ya kilace Wadinnan, domin mutanensa ne na kusa sannan abincin da za'a kawo daga gidan su amaryarsa yake so a kawo masu su, dan na jama'ar da aka yi ya tabbata da wahala a dadada masa rai, duba da ba kowa ke maraba da auren nasa ba Da kula ya masu ja gaba har baban falon, yan matan amaryar saura sunne a gaba, sai Rauda dake rike da wani kula madaidaici tana tafiya cikin yannayinta na sanyi sanyi da kuma tsarin salon tafiyar da Allah ya haliceta da shi har ta karaso kan dokin kofar daidai direba zai juya da kula ta ce" Baba kar ka yi nisa, ba jimawa zamu yi ba" Angon ne da kansa ya juyo yana fadin" Haba aminiyar aminiyata, ya koma idan muka gama ci sai a maidaku gida ko?" Ajiyar zuciya ta sauke ba dan ta so ba tana jin dari darin shiga falon, bata yi tsamanin a falo zasu samu angwayen ba maimakun filin gida, sai dai bata ki shiga ba gannin ba ita kadai bace mace a cikinsu, kuma ita dai ba jimawa zata yi ba gaskiya Takalminta ta cire a kofar dakin, kasa kasa tana binsu da kallo ta yi salama sannan ta sako kafarta mai haske da tsafta tana taka tiles din ta nufi wajen da aka ajiye abincin ta ajiye coolar ta sake juyowa dan neman wajen zama Idannuwanta suka sauka cikin na Ishak da Nafisa Shi Ishak din ba zata iya tantance kallon da yake yi mata ba, ama na Nafisa zata iya ajiye shi a matsayin kallon jin haushi ko na laifi? Allah masani, abinda take hangowa dai kamar tarin jin haushi ne, ta yiwu laifi ta yi mata bata sani ba? Ko ita dinma a wajenta bakin jinnin ta dauko? Dan kuwa ta kasance budurwa mai bakin jini a cikin yan mata, ba kowace budurwa ke mata magana ba, akan ce wai ta cika girman kai , da sauransu, ita kuma tana rayuwarta ne daidai misali Kujerar da ta nufa da nufin zama ce ta ga wata tanfatsetsiyar waya ajiye, a hankali ta dauke dubanta ta dan juya dan zaunawa a wani wajen tana dan sakin murmushin abokin ango na mata tayin gefensa Idannuwanta ne suka sake sauka bayan wani saman salaya, hannayensa harde a kirjinsa, kansa sade kasa , a hankali ta dauke dubanta a kansa ta juya ta karasa saman kujerar dake facin din wace ke dauke da wayar ta zauna ta maida dubanta wajen angon dake miko mata ruwa na cikin jarka yana mata fira a ranta kuwa ta ayana' Na tsani na ga namiji har namiji yana Sallah a daki, dan rashin mutunci ko yana aikin uban me aka yi sallar aka barshi?' Salamce sallarsa ya yi a hankali ya sada kansa yana addu'a har ya gama ya shafa sannan ya mike ba tare da ya kalli kowa ba ya nufi wajen zamansa ya dauke wayar dake ajiye ya zauna yana sake hade rai gannin natacen kallon da yan matan nan suka bi shi da shi, kai subahanalah ya ki jinnin irin wannan hadin da ake yi yan mata da maza, su ba yara ba, ba komai ba ama sai a hadu wai a ci abinci a biya yan matan su tafi, shi kam idan ya tashi dauko hudun nan ba za'a yi wannan badalar da shi ba, yan matan kowace zata yanka ainahin abinda take so a biyata sai a biyata ba sai an zauna ana rainawa junna hankali ba Dubansa ya kai wajen daya daga cikin abokan ango mai sunna Idriss a lokacin da ya miko masa ruwa yana fadin" Biya maradi Allah dai ya kaimu ranar aurenka, a wannan rana ban san wa zai iya amsa sunnansa ba, Allah ya karra lafiya namu" Yannayin fuskarsa bai cenza ba daga daurewar ya amshi jus din ba dan zai sha ba ya ajiye gefe kasa kasa ya ce" Ku salame su mana bafa ba son damuwa" A lokacin da yake furta kalmar "ku salame su mana...." a daidai lokacin ne ya sauke dubansa a kan wace take face da shi tak tak kamar an ajiyeta ne hankalinta sam ba a kan kowa ba, tana rike da goran ruwa bata bude ba , kuma bata ajiye ba Dubansa ya so daukewa tashi daya daga kanta, sai ya samu idannuwansa da dawowa suka sake sauka a kan fuskarta a daidai lokacin da take karanta sakon Bara'atu wace mijinta ya sanar mata mutuniyarta fa gatanan ta daka fuska bayan harda biya maradi a taron, shine ta mata msg din da ya sakata sakin tautausan murmushin da ya saka gefen idannuwanta kadan suka lotsa hancinta ya sake dan budewa kadan sai kuma ya koma yannayinsa saboda gimtse murmushin da ta yi ta dago dubanta a hankali ta kai kan angon kasa kasa ta ce" Kai ko?" Dariya angon ya yi yana fadin" Eh, ba zaki dago mu yi fira ba? Zan kuma kai kararki ne " Murmushi ta yi tana dauke dubanta ta juyo da nufin kallon hanyar kofa, dan mamaki ke neman kasheta na abokanan tafiyar tata, yaya za'a yi su zo waje su wani saki jiki haka a gaban mazan da basu sani ba su ringa fira haka da iya yi? Tun ba'a ce su raba abincin ba har sun bubude sun shiga zubama abokan angon a plate plate sai wani irin iya yi suke yi da Gwali, ita abin har daria ya so bata, ina ajin? Ina jiji da kan? Zamani ya zo mana da sabon salo mai wuyar fasara, ace yanzu mace itace zata yi iya yin da namiji zai gane ta? Lalle wahala bata bar wasu matan ba, WALAHI tsakaninta da namiji sai dai ya bita ba dai ta bi shi ba! A hankali idannuwanta suka sauka a kan fuskarsa, sai dai abin mamaki ko second biyar bata yi tana kallon gefen da yake zaune ba ta dauke kanta tare da nunin alamun bata san da zaman dan Adam a wajen Bama bale ya isheta kallo Mamaki ya kama shi mai girman gaske Har angon da wanda ya sanarwa a salami yan matan suka dawo dan waje ya ja shi ya sanar masa sakon *YUSEF* din cewar a salami yan matan nan baya son takura Rasa yadda zai yi ya yi, a dole cikin murmushi da basu daraja ya ce" Amare, har kun fara raba abincin? Ai da baku ba kanku wahala ba, so nake a maida min ku da wuri ku shirya min hajiata a kawota da wuri wuri, sai kuma na ga har kun fara hidima da mu? Nafisa ce ta yi gagawar dagowa tana sakin fari hadi da murmushi ta ce" Haba elhajinmu, ai ba dawainiya, an riga an zama daya, mun fara ai bari mu gama ku ci idan kun gama sai a maidamu, amaryarka kar ka damu kaima ka san tana hannun manya dole ta sha gyara " Sai da ta dasa Aya Rauda ta dago da mamaki ta zuba mata ido A hankali ta lumshe idannuwanta ta maido dubanta kan Elhaji, yannayin muryarta kasa kasa sannan da sanyin nan ta ce" A'a , a maida mu ya fi, sai ku samu sarari ku ci abinci cikin nutsuwa aminin aminiyata" Da sauri Nafisa ta juyo tana kallonta, duk yadda ta so Hanna kanta nuna bacin ranta sai da ta ce" Mu zamu Hanna su sakewa ne? Ko dama an taba yi basu ci abinci ba mu mu juya? Me muka yi Kennan?" Rauda ta sake tsareta da duban dake nunin abinda ke cikin zuciyyarta, ama bata yi magana ba, sai da ta sake bude baki zata yi magana sai ta ga Rauda din ta mike hankalinta kacokam a kan angon da ido ta masa alamun ita fa tafia take so bayan fuskarta ta wani irin nuna lalaci irin na shagwababen yaro , sannan ta masa nuni da agogon hannunta siriri mai ruwan zeba cewar lokacin ta tafi ya yi Daga yadda yake ya sake dagowa ya zuba mata ido a tsayen da take tun daga yalolon jan mayafin dake yafe saman gashin kanta har zuwa yatsutsanta masu ɗauke da abin lalle irin na mata Kansa ya sake daukewa ya kai dubansa kan Ishaq, sai ya ga shi din ma shi yake kallo da kuma wannan dake tsayen Elhajin ne ya samu da dabara ya nunawa su Nafisa ai ba komai sannan ya rako su har wajen motar dake parker ya mikawa kowace embulop da ya zo kan RAUDA ya miko mata Tata du ta fi tasu girma da alamun ta fi tasu nauyi yana fadin " sai mun hadu da dare wajen kawo min aminiyar ko aminiyar aminiyata?" Murmushi Raudat ta sakar masa tana ajiye kudin da aka bata saman cinyarta a saman labanta ta furta" In sha Allah" Direban ya ja su, matashi da shi irin matasan nan masu zuciyar nema dan yaro ne a shagon Elhajin , haka kuma direbansa ne da gidansa baki daya A lokacin da motarsa ta tsaya bakin Danja kunnayenta suka ringa jiyo mata shewace shewacen su Nafisa dake baya, ama sam bata jin abinda suke fada har sai da motar ta tashi suka dauki hanyar gidan bikin kasa kasa ta jiyo magana kamar haka" Ke kuwa, meye a ciki banda gayar tsiya? Itace fa jarin matar marin nata, shi kuma marikin mashayi ne kuma mazinaci!, Wai nan bikin aminiyarta ake yi ta kusa da kusa ama bakin ciki da bakin hali ya hannata ta yi kwaliya irin na sauran yan mata, ki duba ki gani sai hade rai da jiji da kai na banza , isar baka isa ba, ita ba yar kowa ba sai kwonbo da gashi da kuma kirar nan wace a wannan zamani du mai son ajiye kira irin nata tsaf zai ajiye in ya shiga wajen masu magani, aikin banza bata san yanzu maza yan kyale kyalen yan mata ke jan su, ba wai ire irenta ba?" Kanta ta dauke , bata da niyar tankasu, har wace ke maganar tare da Nafisa ta ce" Asalamu alaikum jama'a....mun zo maku da nagartacen ingantaccen maganin Ulcer, magani ne na Hausa jikake wanda Dubai suka gwada suka ji dadinsa, nagartatun tsatatatun itaciyoyin da suka bamu sasake masu anfani ne ake anfani da su, a nan jamhuriyar Nijar a garin Damagaran a farashi mai rahusa dubu biyu yan naija , yan nijer kuwa 1500francs mai bukata ga numbar +227 96897192 , HAJIA RAHAMA 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *AZAL!* 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *SAJIDA NIJAR* *PAID BOOK* _Bismillahir rahamanir-rahim._ *3* *wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nigar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍* *TALLAH, TALLAH, TALKAH* _*TOH TO TO!*_ 🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_ _Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_ Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake _Amarya_Uwar gida_ _Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_ _Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_ INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼 🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI* *🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU* _KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_ _SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_ 💁🏽‍♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻* 💁🏽‍♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI… _MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_ *ADRESSE 94536935 94.53.69.35* *Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER* KARKU BARI A BAKU LABARI🥳 Litattafan marubuciyar Duk karyar kada Yar mahaukaciya Bak'a ce Bani da zabi Daga tafia daukar soja Neman na kaina Kutkale Mage Bani da zabi Idan ka raina inda kake Umughuluk itifal Duk nisan jifa Wata kokowar Ni zan ladabi Dakika biyar Da ciwo a zuciyata Aure yakin mata Alkalamin Kadarata Dutse Daga tafiya daukar soja Makauniyace ND now *AZAL* Kanta ta kawar, bata da niyar tankasu har wace ke firar tare da Nafisa ta ce" FIFI, wai dan Allah baki ga irin yadda mijin aminiyar Tata ke kure mata waje ba? Ke kudinta fa ta yiwu ya fi namu yawa!" Nafisar ta ja dan tsaki ta sake rage murya, domin magana ce suke yi kasa kasa sosai dan kuwa direban dake jan su ko kadan baya jin abinda suke fada , ama ita Allah ya mata karfin ji shi yasa dukkan furucinsu a kunnayenta, kasa kasa Nafisa ta ce" Na zaki gane ba, wannan fa da kike ganninta babbar yar hannu ce, idan kin ga tarin samarinta sai kin sha mamaki, ba za'a ce a'a ba in akace shima yana soyayya da ita din, bata da haram fa, kuma tsaf zata rabaki da saurayinki sai dai ki yi hakuri, gashi ita iyayenma bata da su bale a kai kararta wajensu, iyayenta hatsari suka yi suka mace harda yayarta da kannunta uku, ita dayar nan uwa maya suka bari a hannun kannin mahaifinta, shi kuwa baya hanawa bale sakawa, inma ka kai masa kararta tsaf yake iya daure mata, Ni dai abinda ba zan lamunta ba da ta wulakanta Ishak, ban san waye ke son numbarta ba na amso na bashi ta wulakanta su, ko ji take ba zata samu biyan bukata a wajensa ba?" Da ido dayar ta saci kallonta, gaba take ama tana iya fasara yannayinta, a gaskiya a yanzu da take zaune ba kwaliyar a fuskarta ana iya daukanta a bar su, su da suka shafa hoda da ja gira da su jan baki da gashin ido, to ita gashin idannuwanta kadai sun isheta, danma ba fara bace cen cen din nan, ama yannayin fatar jikinta tamkar ta yan Ethiopia wankaku masu rantsatsen hutu, kai kamanunta kansu tamkar wace ta samo usuli daga su, saima hannayenta da kaffafuwanta, sunna da tsafta da kyan kallo, hannayenta kuwa harda yan faratuna take tarawa na ra'ayi mikaku farare tas tas da su, tana dauke da quality masu fuzga, ba wai manyan duwawu ne da ita ko manyan breast ba, a'a, komai dake jikinta ne dan daidai da tsarin halitar jikinta, sai kuma ta iya saka kaya da wasu yannayin dake daukan hankalin har mata ba iya maza ba, sau tari idan ta halarci taron mata kawai zaka ji ana tambayarta wai gashin idon nan nata ne? Wai me take shafawa? Dan Allah me take anfani da shi a lebenta? Dan Allah yaya take yi kaffafuwanta da hannayenta suke haka cikin tsafta? Sai dai ta yi murmushi tace haka Allah ya haliceta, kuma haka din ne , sai dai wanka kawai da ta karra, ko kwali na koda yaushe take sakawa ba bale kwaliya, ama a haka din dai take da nata farin jinin da ya tsolewa wasu ido Kasa kasa kawar Nafisa ta ce" Fifi gaskiya Atu ta yi sake, Ni idan nice ba zan taba amincewa da haka ba gaskiya, cap, wannan ai sai ta kwace min mijina ina ji ina gani" Daidai motar ta tsaya kofar gidan su Bara'atu , direban ya sauke madubai sannan ya cire masu sakatar motar A Nutse ta bude bangarenta ta fito sannan ta je gefen da suke ta saka hannu ta bude masu ta kuma tsaya a kan hanyar fitowar ta saka idannuwanta cikin ma Nafisa, wace sai da gabanta ya fadi ta dan samu kanta da dan ja baya tana kallonta lokaci daya tana fadin" Ke kuwa lafiya?" Rauda ta bi su daya bayan daya da kallo, sai kuma ta saki murmushi, cikin yannayin da zaka rantse ba zata iya furta wata kalma sama da hakuri ko hailala ba ta ce" Kina da matsala da Ni ne?" Ba yan matan nan kadai ba, hatta direban nan sai da ya juyo ya zuba mata ido, domin a yanzu ras yana ji dan ya tsayar da amon rediyon motar Nafisa ta sake dubanta da mamaki ta ce" Wai da Ni kike RAUDA?" Rauda ta lumshe idannuwanta da wani yannayi ta daga kafarta ta saka cikin motar sannan ta janyo kofar ta rufo da karfin tsiya ta juyo bayan ta ajiye wayarta a aljihun motar tana kallon yan matan gaba dayansu ta ce" Da ke, da kuma ku nake, Akoy mai matsala da Ni ne? Mu warware ta saboda bana son kwonciya da tunanin wani banza, nace inada matsala da ku ne ta yadda zaku ringa wulakantani a gabana?!" Ta karashe a kausashe tana juyowa gaba dayanta Direban ne da sauri ya shiga yana fadin" HAJIA, kin ga kar ki kula su sauko ki yi tafiyarki, ko me suka maki ki yi hakuri kin ji?" Nafisa ta cafe maganar tana fadin" Karma ta sauka, ta yi mana abinda zata yi!, da ke din nakkkkkkkkkkkkkk" K din kawai ya dan fito a karshen furucinta ta samu kanta da dantse harshenta lokaci daya sakamakon dauke fuskarta da Rauda ta yi da mari sannan ta rike mata wuya harda kokarin daneta a cikin motar Ihu suka kwasa sauran yan matan biyu suka shiga kokarin kwantar Nafisa, sai dai gannin abin na neman zuwa kansu dayar ta bude motar ta fice tana haki har takalminta ya cire saboda yadda ta fito daga motar hankali tashe ta sake duban Nafisa dake kai duka a iska bata samun Rauda din, ita kuma Rauda har idannuwanta sun juye ta rike mata wuya taf tamkar wace zata aikata kiyama Gannin za'a yi kisa ya saka shi fitowa da sauri ya bude bayan ya damko Rauda ya fizgota da dukan karfin da Allah ya bashi, ama cikin ikon Allah sai da ya wartota da dan kunnen Nafisa guda wanda ya yi fitar karfi ya janyo ya ja mata shatinen da ya farke mata da jinni Kusan a tare suka saka ihu, shi direban da Nafisar da kuma dayar kawar da ta kasa fita saboda gaba daya Nafisa kanta ta dane garin fadan Mutane tuni sun fara taruwa a wajen motar a lokacin da ta warce jikinta ta sakar masa harara ta sake ridar motar shi da kansa ya so yin hali irin na mata, wato ya ware muryarsa ya kwala ihun a taimake shi, sai ya ga ta janyo wayarta ne da dan yalolon mayafinta Ido tuni sun kade mata ta dubi Nafisa dake ihun ta yanka mata fuska murya a dake ta ce" Ban maki komai ba cikin tarin abinda nake son maki, ba kin ce a ce min idan kika ganni sai kin wulakantani ba? Ni zan fada maki gwa da gwa kin ciri katin fada da Ni mai rabamu sai Allah!, dan na maki alkawarin haduwa goma sai na kawo maki hari sai dai ki kasheni, zan nuna maki mayar nake ta kirki idan na riki wuyanki, haka kuma zan nuna maki mai kwacen mazan mutane nake ta hanyar bin duk wani namijin da zai nuna yana son ki, ke sai na zame maki *AZAL* a rayuwa tunda kika zagar min iyayena!, sannan ki je ki sake bincike labarin da kike da ba daidai din bane karamar yar is....." "RAUDA?" Muryar mahaifiyar Atu ta katse ta Tun daga kanta har kafarta dake ja ba takalmi ta bi da kallo sannan ta karaso da dan sauri tana yiwa ya'yan Atu magana kan ya watsa mutanen dake neman yin taron idi a wajen ta sake zubawa Rauda ido sannan ta leka motar da kuka da ihu ke tashi Sai da ta tsorata gannin yadda jinni ya BATAWA Nafisa atamfarta da fuskarta A tsoracen ta ce" Subahanallah, innalilahi wa inna ilaihi raj'une, menene duka wannan? Yanzu RAUDA dama baki daina fada irin wannan ba? Me ya yi zafi haka? Kai Usman maza fitar da mota a kai wannan asibiti, ke kuma wuce mu je ciki wuce, dan Allah kowa ya tafi ku tafi kawai , du kun tsatsaya an rasa mai kama masa a kashe fitinar nan sai da ta zama haka? Subahanallah Rauda yau sai na saba maki yau sai na saba maki Rauda!" Nafisa da ake tarewa tana kuka ita kadai ta san me take ayanawa a zuciyarta, abu daya ta sani in har wannan mahaukaciyar ta mata ila sai ta rufeta dan na zata taba yarda ba, ashe mahaukaciya ce bata sani ba? Da ta san bata da hankali na zata taba yarda su shaki iska daya da junna ba, a irin yadda take kafa kafa da jikinta ita ko fada bata taɓa hada jinni da kowa ba, abu daya ta sani in dai tana fada da kai in ta sakoka a gaba da habaice habaice da harare harare har sai ka ji kamar ka daina fita cikin sa'ani, sai gashi tun kafin abin ya kaisu da haka daga magana wannan mahaukaciyar ta mareta hadi da yi mata rauni? Ba zata iya yafe wannan wulakancin ba Rauda kuwa bata tsaya ko'ina ba sai cen kuryar su Atu Tana shiga ta samu waje ta zauna a kasa ta sada kanta Jim kadan sai ga mahaifiyar Atun ta shigo , tun kafin ta zauna ta shiga fada tamkar zata ari baki, fada take yiwa Rauda irin fadan da uwa ke iya yiwa y'arta cikin fadan ya ce" Ashe bakya jin magana? Inace nan ma maku maganar fadace fadacen nan kuka ce min kun daina, shine zaki hada jiki da mace har ki mata wannan raunin? Ina anfanin wannan abin da kika aikata Rauda? Ya Salam me ya haɗa ki da ita da zafi? Me yasa wani lokacin bakya kwabar zuciyarki ne? Ko menene idan kika yi hakuri ba Shikenan ba? Mai hakuri yakan dafa dutse , a matsayinki na mace a kulun fada maku nake yi ko muryarku ba kowani banza bane zai ji kai tsaye, komai na mace abin a kilace ne a ririta, komai naki daraja ne da shi, har wancen ya kamo ki ya fitar da ke daga mota? Ya Allah haba RAUDA " A hankali Rauda ta dago idannuwanta tana kallon maman aminiyarta wace take kira da Mama itama, a sanyaye ta budi bakin da nufin fadin abinda suka yi mata sai kuka ya kubce mata, domin a duniya idan kana so ka ga hawayenta ya zamto zata fadi wani abin da aka yi mata har ya mata ciwo a zuciyyarta A hankali ta iya furta" ban masu komai ba, har iyayena suka zaga" Jikin Mama ne ya yi sanyi sosai, ta sani abinda ya shafi iyayen yarinyar na rikitata sosai, ko dan Kadara mai zafi ta daki rayuwarta ne? Idan abu ya shafi iyayenta bata iya yiwa kanta tsawa ko fada, ama du da haka sai ta ci gaba da yi mata fada mai shige da nasiha hadi da gargadin rayuwa kafin ta umarceta kan ta KWONTA ta huta ta kuma share hawayenta Allah ya sanyaya ya shirya Ta kwonta din, ama bata samu hutun da ya dace ace ta samu din ba sakamakon tinowa da Tata RUBUTACIYAR (litafin KwAte), tabas ta san Tata kadarar mai zafi ce, haka kuma bata cika son tinowa da ita ba saboda a duk lokacin da ta tuna tana iya wuni ta kwana cikin halin kuncin zuciya da bacin rai, kwata kwata bata so hakan ta faru a wannan babbar ranar ba, rana ce ta farin cikin aminiyarta wace ta jima tana hasashen irin wunin farin cikin da zasu yi, sai gashi wata wace bai dace ace ta shiga huruminta ba ta saka ta aiki irin na rashin hankali A lokacin da ake hada haɗar zuwa a dauko amarya daga wajen da take wuni ta samu ta silibe jiki ba kwari ta fice a gidan ta je ta samu dan sahu ta shige ta nufi gidansu A lokacin da mai adaidaitar ya tunkaro gidansu sai ta ji inama ace zata iya samun shiga ba tare da ta hadu da kowa ba? Kai da ta ji dadi sosai Idannuwanta kyam a kan kofar shiga gidan bayan mai adaidaitar ya tsaya ta sauko ta Bude ambulop din nan tana duba kudin ciki ta zaro ta mika masa sannan ta juya ta sake zubawa kofar ido kafin ta sauke ajiyar zuciya ta nufi cikin gidan tana rokon Allah ya sa kar ta hadu da kowa Tana shigowa gidan daidai Farisa na watso ruwan wankin da ta gama tsakar gidan ba abinda ya shafeta da gudun wajen ya cakule Kallon Rauda ta yi daga kasa har sama ta tabe baki ta yar da robar wankin nan cikin rana ta yi shigewarta cikin madaidaicin falon gidan Ajiyar zuciya ta sauke sakamakon jiyo sautin Muryar Farisa tana fadin" Mama ga Rauda nan ta dawo fa, dan Allah ta dora maki girkin Ni na gaji da yawa" Takalmanta take cirewa kunnayenta suka jiyo mata magangannun da suka gama zaunawa a kirjinta masu kayar mata da gaba da hadasa mata bugun bugun zuciya, gashi amon Muryar na Maman matsowa yake yi tana fadin" wace Raudar? Yau da ban ci mutuncinta ba marar mutunci da bata gaji abin ALKHAIRI ba? Ace ana auren a gidan kawar taki masu kuɗi kina babar kawa ba zaki tsaya ki kawo mana abin arziki ba zaki dawo min yanzu? Uban me kika zo dauka a gidan ko dan nice banza da bani da mai tausaya min kika dawo ki ci dan abinda na kurkurta na ajiye? Ina take munafukar banza da wofi wace babu ta sauka a gidansu ta yi ya'ya ta yabanya Shegiya wace ta gaji tsiya?" Kai ta sauke kasa tana sauke ajiyar zuciya hadi da ambaton Allah a cen kasan zuciyyarta sannan ta dago da sauri tana kallon inda Mama ta ja ta tsaya tana kare mata kallo da wani matsiyacin kallo Jiki ba karfi ta ciro ambulop din da aka bata, wace ta amsheta ne dan ta ba Mama ko zata samu ta numfasa cikin Salama, tana rayuwa a gidan nan ne dan tana kawo irin gudunmuwar da Mama ta fi so wato kudi, ba ruwanta da sannin ta hanyar da zata kawo mata, ita dai burinta ta ciro ta miko mata, ba godi bare na gode zata tisa kudin da bata bada abin siyarwar da aka Saïda aka kawo mata ba ta irga ta toshe a harshen zani ta boye ba, dan na ita ta haifa ba bale hakan ya dameta , wannan din itace kadai hanyar da RAUDA ke iya samun abinci a gidansu, gidan kannin mahaifinta , marikinta Ambulop din Mama ta bude ta dubawa, ido ta zarro sakamakon kudin da ta gani a ciki ta dago tana dunanta ta ce" Asalamu alaikum jama'a....mun zo maku da nagartacen ingantaccen maganin Ulcer, magani ne na Hausa jikake wanda Dubai suka gwada suka ji dadinsa, nagartatun tsatatatun itaciyoyin da suka bamu sasake masu anfani ne ake anfani da su, a nan jamhuriyar Nijar a garin Damagaran a farashi mai rahusa dubu biyu yan naija , yan nijer kuwa 1500francs mai bukata ga numbar +227 96897192 , HAJIA RAHAMA 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *AZAL!* 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *SAJIDA NIJAR* *PAID BOOK* _Bismillahir rahamanir-rahim._ *4* *wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nijar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍* *TALLAH, TALLAH, TALKAH* _*TOH TO TO!*_ 🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_ _Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_ Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake _Amarya_Uwar gida_ _Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_ _Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_ INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼 🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI* *🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU* _KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_ _SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_ 💁🏽‍♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻* 💁🏽‍♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI… _MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_ *ADRESSE 94536935 94.53.69.35* *Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER* KARKU BARI A BAKU LABARI🥳 Litattafan marubuciyar Duk karyar kada Yar mahaukaciya Bak'a ce Bani da zabi Daga tafia daukar soja Neman na kaina Kutkale Mage Bani da zabi Idan ka raina inda kake Umughuluk itifal Duk nisan jifa Wata kokowar Ni zan ladabi Dakika biyar Da ciwo a zuciyata Aure yakin mata Alkalamin Kadarata Dutse Daga tafiya daukar soja Makauniyace ND now *AZAL* Ido ta zarro sakamakon kudin da ta gani a ciki ta dago tana dubanta ta ce" Wadinnan kudaden duka naki ne? Ama sato su kika yi ko?" Cikin nauyin harshe da zuciya Rauda ta girgiza kai ta ce" A wajen kai abincin angwaye aka bamu" Ido Maman ta sake kwalalowa tana fadin" Ikon Allah, shi yasa nace maki yau din nan ki dage bakin rai bakin fama ki warto abinda kika samu kar ki yi sake ko kadan a fi ki ci, ke ce fa aminiyarta ta hannun dama, kin ga dalilin auren nan kema sai na fara maki dan tare tunda an mutu an barni da wahala dan ko shi wanda ya dauko ya kawo min ya zura min ido ina ta fama ina faduwa ina tashi, YANZUN me ya dawo da ke gidan tun warhaka bayan ba'a yi mai kankat din ba, ba'a kai amaryar ba?" Da kyar Rauda ke iya daga idannuwanta, muryarta a raunane sosai gaban wace bata iya dagawa murya ta ce" Kaina ke min ciwo sosai, shi yasa na dawo gida dan hayaniyar jama'a ta yi yawa a cen din" Sai da Mama ta yi mata kallon shekeke kafin ta tabe baki ta juya tana fadin" Kin ga, karma ki cire takalmi maida shi, inada panadol a nan bari na baki ki kora da ruwa ki juya, hayaniya ai dole a yi, in banda ɗorawa kai abu kai ba kowa ba kace ba za'a yi maka hayaniya ba, ki wuce kawai ki koma dan WALAHI na tabbata tunda yanzu kika samu wannan wanda zaki samu in an jima sai kaina ya kule wajen irge" Tana fadi tana nufar dakinta ta dauko maganin da ledar ruwa daya ta dawo ta fasa ta mikawa Rauda dake tsaye har kamar juwa zata bugata da kas ta ce" Sha maza juya ki koma " Jiki ba karfi ta hadiyi maganin cikinta ko abincin kirki babu a ciki ta juya tana langwui ta nufi kofar gidansu kunnayenta na jiyo mata Maman na fadin kar fa ta dawo da wuri sai an karkare komai an gama........, wannan din itace kalar rayuwar da take yi a gidansu, gidan kannin mahaifinta, wanda ya je ya daukota a wajen cousin sister din mahaifiyarta tana cencanarta daidai karfinta yana fada yana komai yana fada mata cewar shine gatanta shine dolenta bata da wani uba sai shi bata da wani dangi sai shi yana raye ba zata je gidan yar uwar yar uwa ta rayu ba, sai dai kashhh, eh lalle uncle dinta mai zuciyar yi ne, ama kuma tasa jarabawar rayuwar shine shaye shaye, idan akace wata ya kai karshe dama ba mai nemansa, gaba dayan yan kudaden na aikin yake kwashewa ya je gidan giya ya yi zamansa ba za'a kuma ganninsa ba kuma sai ya cinye abinda ya samun ya fara rasa abinci sannan zaka ganshi a gidan , wannan dalili ya sa matarsa ke Tata rayuwarta itama yadda ta yi niya, eh lalle da nemanta ake dora tukunya a gidan, ama kuma wani barin ta maida yar rikonta jarinta, dan a mutu ko a yi rai sai Rauda ta nemo mata kudin da bata dora Mata kayan sana'ar nemowa ba, idan bata kawo ba zata riski wulakancin rayuwa ita da yaron uncle din nata wanda mahaifiyarsa ta rasu ta bari mai fama da tabin hankali, kusan a gidan Allah ne gatansa sai ita dake fama da ragamar hidima da shi ta yau da kullum, wahalhalunsa kadai sun isa su sakata a wani hali duba da shekarunta da kuma kasancewarta mace, sai ga wahalar da ta fi kowace , wace kiri kiri take gane Yaren marikiyarta in har bata kawo mata ba komai na iya faruwa ciki harda korarta, shi yasa take tafiyar da rayuwar ta tsakaninta da maza masu sonta ba jin tausayi in dai ba zaka bata ba dama kai din ba abokin tafiyarta bane, bata taɓa sakawa ranta zata auru ba, shi yasa take tafiyar da rayuwarta yadda hali ya bada,.....cikin kudira ta Ubangiji a haka din har yanzu bata bankadar da kyauran da ake yi mata kallo ba, sai dai ita da kanta ta san da wahala har ta bi iyayenta da kanninta kiyama ba tare da ta barar da mutuncinta ba, duba da yadda yannayin ya koma yanzu tsakanin samarin da yan mata bani in baka ne, da wahala ka zauna zance da saurayi ba tare da ya kawo maka lalata ba! A sanyaye ta karasa bakin titi ta tari san sahu ta masa kwatancen gidan su Bara'atu bayan ta saka hannunta a rigar Mamanta wajen da ta boye kadan daga cikin kudin da aka bata dan ta samu na cin abinci idan an Hanna mata ta kuma siyawa yaron wajen uncle dinta ta ciyar da shi koda a boye ne dan yawancin lokuta idan tana cikin punition har shi shafa take yi, dan abincin da ake zuba masa a robar nan blue ta almajiri tsaf ake iya Hanna masa ace abincin ya yi kadan A lokacin da suka karasu tuni ana cikin gidan ana ta haramar daukan amarya wace ta rikicewa mahaifiyarta da tambayar ina RAUDA? Mahaifiyar Tata kanta ta nemeta ta rasa har ta shaida mata ga inda ta barta , wato a dakinta tana barci A karro na bakwai Kennan Atu ta kuma kiran layin Raudar, nan ta ci Sa'a ta daga kiran tana kokarin daidaita muryarta a sanyaye sosai ta ce" Aminiyatahhhhhhhhhh, yau zan kai aminiyatahhh dakinta" Atu dake ta rike hawayenta a hankali ta sake su tana sauke ajiyar zuciya gannin Rauda ta daga labulen falonsu ta shigo idannuwanta a kanta Soyayya Allah ne ke haɗawa, zumunci Allah ne ke haɗawa Atu ta fi RAUDA komai na rayuwa, kama daga jin dadin gaban iyayen har zuwa yannayin halitta dan kuwa ba laifi Atu jinni ce ma larabawa gaba da baya, ama Allah ya saka mata soyyayar aminiyarta a zuciyyarta kamar yadda Allah ya tankwaso zuciyar RAUDA duk irin yadda ta cinkushe da sama da kasar rayuwa ta samu budewa Atu take rayuwa da ita tamkar y'ar uwarta ta jinni, aminiyarta da zuciya daya Sunna da alkawaririka a tsakaninsu masu girman gaske, haka kuma sunna iya yinsu san gannin zumuncinsu ya haifa masu abu mai alkhairi duniya da kiyama A hankali ta zauna daf da ita, a sanyaye sosai Atu ta dora kanta da ya sha sarkar nan ta larabawa saman gashinta wanda ya sha turare da nadin lafaya a gefen kafadar RAUDA kasa kasa ta ce" Kin san kafarki kafata? Na zan taba yarda na je na barki ba" Murmushi Rauda ta yi wanda ya ratsa har zuciyyarta, a sanyayan itama ta ce" Kin san ba'a taba yin haka ba? Karma ki rakito mana rikicin da bashi da anfani" Dagowa Atu ta yi tana kallonta ta ce" Kar mu yi haka da ke, na sh fada maki in dai bamu yi aure tare ba idan na rigayeki sai dai ki tare a gidana, nima haka ko?" RAUDA ta dan kwalalo ido kasa kasa ta ce" bana son iskanci fa " Atu ta hade fuska ta ce" Ni shi na fi so, me zaki yi a gidan cen? Bana sonki a cen" A hankali RAUDA ta dan zuba mata ido, sai kuma ta yi gagawar kawar da tunaninta, domin da farko ta so ta sanar mata abinda ya faru yau dinma, dan a duniya Atu ce kadai halitar da take tardowa da zafi zafi ta sanarwa damuwarta, sai dai yau ba ranar ta daga mata hankali bane, sai kawai ta wayance ta mike tana fadin" Bani da lokacin shirme irin na auta, bari in idasa harhada maki komatsanki dan mun kore ki fa, ba kuma zamu sake karbar shirginki ba yanmata " Ita dai Atu wata Salama ta samu a cikin zuciyyarta, Duda yanzu suka gama hawa sama da faduwa da kanwar mahaifiyarta a kan RAUDA, Tati ta nunawa mahaifiyarta bata son kusancin Atun da RAUDA, wai yanzu duniya ta lalace , yaushe rabon duniya da ƙawance, har ta karɓe tarin suturun da Atu ta warewa Rauda zata bata tace ba za'a bata ba, duniya ta lalace ta daina tausayin kawar nan Tata tana iya son mata miji, ire iren abubuwan nan dai mararsa dadi, har sai da Atun ta fara kuka sannan ta kyaleta, dan ba zata iya ganewa ba, sam ba zata yarda da irin zumuncin dake tsakaninsu ba, amana daya ce, gamon jinni ne daga Allah, tunda *AZAL* ta fada ratuwarta RAUDA ta rufa mata asiri bata tunanin a nan duniya wani abu zai rudi Rauda ta wukakantata ba, wai ba maganar miji bane ake yi? Su auri miji daya har zuciyyarta ba zata yi bakin ciki ba, tana son RAUDA domin Allah kamar yadda itama take sonta Bayan sallar isha i aka shiga hada haɗar tafiya da amarya A cikin motar da aka dauko amaryar mutun uku ne kawai a ciki, amarya, gefenta auntynta kanwata mahaifiyarta sai RAUDA a dayan gefen tana rike da hannun amaryar sunna magana kasa kasa tana ta rarashin Atun kan ta daina kukan hakanan dan sun sha kuka tare har kamar zata kamu da ciwon kai Anguwar jan gwarzo ne gidan Bara'atu, da yar tafia kafin ake isawa, motarsu na shiga gidan aka datse taron mutanen dake waje dan mutanen sun yi yawa sosai gashi an shigo da amaryar A Nutse Teti cike da isa irin ta uwar amarya ta ce" Direba, bana son kowa a hanyar dakin yarinyata, idan na shiga da ita dan Allah a dakatar da kowa, bana so kowa ya shigo, idan nace kowa ina nufin kowa da kowa!" A lokacin da take wannan bayanin RAUDA kadai ke jinta, ita Atun hankalinta na wajen mutanen dake tare tana mamakin karar da aka masu, yawanci kuma saboda RAUDA aka masu wannan karar A hankali RAUDA ta dauke dubanta daga kan Teti, tana iya cewa ta jima da Sannin matar bata son zumuncinta da Bara'atu, Akoy lokutan da kiri kiri ta nuna bata son zumuncin nan nasu saboda yanzu ba'a kawar arziki, a lokacin ta daukewa Bara'atu kafa da gidansu sai da mahaifiyarta ta sameta da kanta ta mata fada ne suka koma kamar da, a kulun idan ta ga irin haka takan jadadawa ranta Adu'ar da take yi wace ta tabbata Allah ba zai kunyata mu'amalarsu ba domin saboda Allah take tare da ita, a yau in bata yi farin cikin ci gaban Atu ba , ba zata zamo mai bakin ciki ba, Atu itace yar uwar da ta rasa, itace wace take fadawa damuwarta ta yi kuka ta share nata hawaye A hankali ta samu ta silibe daga cikin kawayen makarantar su har ta samu ta fito bakin baban titi cikin nutsuwa ta shiga takawa a kafarta, ba dan bata da abin hawa motar komawa gidansu ba, a'a sai dan fatanta Allah ya sa idan ta isa Mama ta yi barci Shikenan ba sai ta tisata da cin zarafin da ta saba ba Tun kafin ta fito daga Anguwar su Atu, wato gidan da aka kawota aure wasu motoci biyu suka shawo kwanar masu shegen daukan ido da kyan gaske Bata yi zato ba sai gani ta yi sun tsaya daf da ita, hakan ya sa ta dakata dole da tafiyar da take yi , tana kallon motar A lokacin da madubin baya ya bude idannuwanta suka sauka a fuskar ango murmushi ya bayyana a fuskarta ta ce" Kar dai kace min har an rako ka?" Shima cikin barkwoncin da suka saba da junna bayan ya roki amini kuma aboki a wajensa kan sai ya zo rakiyarsa har yana fadan kar ya tsayar da shi zai je gaisar da HAJIA yau , sai kace auren farko yace da shi eh lalle ba auren farko bane ama soyayar farko ce dan Allah ya raka shi, sai gashi kuma ya tsayar da su a bakin hanya wai ga aminiyar amarya ko me? Shi yasa ya gama cika fuskarsa ya zuba masa ido shima yana jira ya gama wulakancin su tafi Dan murmushi ya yi ya ce" To yaya zan yi da raina aminiyar aminiyatah, ban gane ba har kin taho baki tsaya kin kwaci budar kan ba?" Murmushi ta saki yanzunma, cikin tsarariyar sanyayar muryarta ta dan girgiza kai ta ce" Wannan ai ka san koda ban kwata yau ba bashi ne, bana so na yi dare ne na rasa abin hawa daga nan zuwa gidanmu" Daya daga cikin abokan su dake gaba ne ya leko shima cikin shigar tasa gizner sai kanshi suke ya ce" A'a haba aminiyar aminiyar aminina kin san dai ba zamu bar tsaleliyar budurwa irinki neman abin hawa ba, me anfaninmu? Shigo Mu je idan muka ajiye shi da kaina zan kai abata nima gida ko?" Tunda suka fara kyarkyarar kamar yadda ya ambaci abinda suke yi a gaban karamar yarinyar da muryarta ya saka shi fasarata haka baima gane ta dazu da rana bace ransa ke kuna har sai da ya ji wani balagagen rashin da'a wai ta shigo su je ya saka shi kallon na gaban da duban hakan ba zata gyara ka ba sannan ya dan kalli angon kasa kasa ya furta" Bana son bata lokacin mu je mana"......ya karashe yana sauke idannuwansa a kan fuskarta a lokacin da itama ta kalli tasa fuskar dan sarai yannayin magana a kamilancen da jimula ta rashin mutunci ta mata kama da ta wanda yace a kore su dazu baya son surutu, ai kam tana sauke idannuwanta suka sauka a fuskarsa , kasancewarta mai baiwa irin ta ji ya saka abinda ya fada tsaf a cikin kunnayenta, har ya zamo a yanzu ta kasa hadiye yannayi na harara da watsarwa da idannuwanta suka dauko sannan ta kalli angon bayan yi murmushi kasa kasa sosai ta ce" Zan dawo ne, kar ka kakabe aljihun dan nawa bashi ne" Daga haka ta juya ta mikar da tafiyarta dan gaba daya nunawa ta yi bata ji Yaren dayan abokin angon ba "YUSEF Please kar ka fita mana" Elhaji ke fada yana kokarin Hanna shi fita a motar dan takaici su ya saka shi saka su tsayawa da nufin zai fice Idannuwansa ya dan lumshe kasa kasa ya ce" Zan zo fa, ka ga zan je har wajen su Elhaji ne bana so na cika dare" A dole Elhaji ya bar shi yana kallo har ya bude dayar motar ya shige baya, motar dake dauke da yan mata biyu , sai abokinsa da kuma direbansa suka dauki hanyar Fada Ajiyar zuciya Elhajin ya sauke yana fatan ganin ranar da amininsa zai daina wasu halayan da suka zamo basu da anfani a duniyarsa, a matsayinsa da darajarsa sam basu kamaceshi ba, sai dai abinda za'a fasara ahalin nasu da shi menene , shin *AZAL* ya sauka a gidan nasu, ko karfin jinnin dake yawo a jikinsu ne ya jaza haka? Rayuwar dai gatanan kowa da tasa a boye, shine uban garin nasa ba boyaye bane tunda ba ubanda yake tsoro! Asalamu alaikum jama'a....mun zo maku da nagartacen ingantaccen maganin Ulcer, magani ne na Hausa jikake wanda Dubai suka gwada suka ji dadinsa, nagartatun tsaftatatun itaciyoyin da suka bamu sasake masu anfani ne ake anfani da su, a nan jamhuriyar Nijar a garin Damagaran a farashi mai rahusa dubu biyu yan naija , yan nijer kuwa 1500francs mai bukata ga numbar +227 96897192 , HAJIA RAHAMA 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *AZAL!* 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *SAJIDA NIJAR* *PAID BOOK* _Bismillahir rahamanir-rahim._ *5* *wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nigar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍* *TALLAH, TALLAH, TALKAH* _*TOH TO TO!*_ 🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_ _Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_ Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake _Amarya_Uwar gida_ _Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_ _Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_ INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼 🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI* *🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU* _KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_ _SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_ 💁🏽‍♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻* 💁🏽‍♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI… _MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_ *ADRESSE 94536935 94.53.69.35* *Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER* KARKU BARI A BAKU LABARI🥳 Litattafan marubuciyar Duk karyar kada Yar mahaukaciya Bak'a ce Bani da zabi Daga tafia daukar soja Neman na kaina Kutkale Mage Bani da zabi Idan ka raina inda kake Umughuluk itifal Duk nisan jifa Wata kokowar Ni zan ladabi Dakika biyar Da ciwo a zuciyata Aure yakin mata Alkalamin Kadarata Dutse Daga tafiya daukar soja Makauniyace ND now *AZAL* A lokacin da Rauda ta karasa gidansu dare ya tsala sosai, ama kofar gidan a bude take ham, hakan ya sa ta gane cewar Uncle dinta ya dawo gida yau Ajiyar zuciya ta sauke a lokacin da ta ganshi zaune saman kujera yana kallon kofar shigowar Karasawa ta yi inda yake zaunen tana dubansa da kula ta ce" Barka da warhaka Abu" Yannayin da yake ciki na damuwar gannin dare na neman tsalawa bata shigo ba bai gushe a fuskarsa ba ya ce" Daga ina kike yar gidan Abu har dare ya yi haka baki shigo ba? Tara fa je neman yi" Ajiyar zuciya ta sauke, tana ji a cen kasan zuciyyarta tanada wanda idan yana cikin hayacinsa yake tunawa da ita, tanada wanda ke damuwa da shigowarta in har yana cikin hayacinsa A sanyaye ta ce" Ka manta yau ne auren Bara'atu? Daga kaita muke Abu" Ajiyar zuciya ya sauke mai nunin ya samu salama a zuciyarsa a sanyaye ya ce" Raudana ki yi hakuri da yannayin rayuwa kin ji? Ki ci gaba da sakani a addu'a, kin ga wannan lokacin ban kashe kudin ba na dawo da na tuna da ke da kanninki, in sha Allah Ni na san zan daina abinda nake yi na zo na kula da ke, ki kama mutuncin kanki kin ji yar gidan Abu?" Idannuwanta ta ji sun cika da kwallah ya Allah, inama ace ta wayi gari bafanta ya daina dukkan rayuwar nan da yake yi ta wulakantar da kai? Da sai ta fi kowa farin ciki, kuma tana kyautata zaton samun yanci irin na wasu ya'yan masu yanci, sai dai kashhh, haka yake fadi kulun, kuma Adu'ar kuwa yi take yi, ama ko yanzu alhamdulilah mutumen da idan ta yi zafi za'a kawo shi a watsar ya sha bashin giya yau har ya riko cenji? Kwonci tashi wata rana ana iya wayar gari a ga ya daina abinda yake yi din, babu abinda addu'a ta bari da izinin mai duka "Nima burina ki samu miji na maki aure, in sha Allah kafin na mika ki dakinki sai na daina shan komai kin ji Raudana?" Rauda ta sakar masa murmushi ta mike ta shige a hankali ta fitar masa da yar yololuwar katifarsa ta shinfida masa sannan ta koma ta dauko sangenta ta daura masa ta masa sai da safe ta shige dakinsu ita da kannin nata ta raba ta KWONTA ko tufafinta bata cire ba, dan burinta ta samu hutun dake hadasa mata ciwon kai, sosai kanta ke ciwo rashin gata ya sakata bin rana dan nemowa Mama kudi _______________________________ Fada Tunda aka sanar da shigowarsa fadar ya saka duk wani mai motsin kai daidaita kansa Ba harkar kowa zai shiga ba, ama kwarjininsa da jinnin dake yawo a jikinsa ya saka duk wani marar ji ke kama kansa idan zai shigo gidan koda na second daya ne Gannin motocin dake parker ya saka shi dan tabe baki ya bude motar ya fice da hannunsa ya yiwa su Ishak alamun su zauna a ciki kar su fito, dan mahaifinsa na nan , ko me yake tsakaninsa da kakarsa ba zai so mahaifinsa na fada baya ji ba Bai damu da muryoyin da yake ji sama sama kadan na tashi a baban falon ba Ya dana kai yana salamar da shi kadai ya ji abinsa a cikin zuciyarsa Hular dake kansa ya cire bayan ya sauke idannuwansa a kan duniyarsa, mahaifiyarsa, wace bai san cewa harda ita a irin zaman nan ba, duba da ba lafiya ne da ita ba kulun cikin ciwo bai yi tunanin tana nan ba da daren nan, tunda ba gida daya suke da sarakuwarta ba wace ta dora Mata karan tsana tana kiranta da lalura ce zama da ita kulun ciwo har ta karra rikita mata yannayi da masifarta, har hakan ya zo ya shigar da fitinaniyar gaba tsakaninsa da ita , dan ba zai taba iya amincewa yana ji yana gani haka na faruwa ba! Bai iya kallon kowa ba sai da ya karasa har daf da mahaifiyarsa ya cire hular kansa ya duka har kasa ya kamo hannayenta da ya ji su dumi sosai ya dora a gefen fuskarsa kasa kasa ya ce" Khalb, me kika fito yi bayan na shinfidar da ke dazu?" Murmushi ne ya subuce mata a saman lebenta, tana kallon yaronta, wai ya shinfideta sai kace yarinyar goye ya dai kofar mata y'a ya sakata hawa gadon dole wai jikinta da zazabi , to bayan fitarsa ne mahaifinsa yace ta fito su gaisar da HAJIA A hankali ta ce" Baka gaisar da mutane ba BIYA MARADI" Sai a lokacin ya sauke dubansa a kan mahaifinsa, wanda shi dinma shi yake kallo da tarin abubuwan dake cikin zuciyarsa Dan musmushi ya sakar masa yana dauke dubansa a hankali daga kansa da girmamawar da ta zame masa wajibi wace mahaifiyarsa ta yi yaki kan dorashi a haka bayan ta fada masa cewar ya guji fushin ubangiji a kansa, babu ruwansa da tsakaninsu, ko me zai mata nasa ido ne babu ruwansa, ama ina, sai da suka yi abinda ya daina gannin girmansu, domin du irin yadda ta ringa gujewa wasu yan wulakanci lokaci zuwa lokaci tsakaninta da su sai da suka ringa yi a gabansa, ya zamto du irin soyayar da kakarsa ke masa shina yake yi mata tsana mai karfi Tata ta shiga zuciyarsa, saboda bata ragawa mahaifiyarsa a gabansa Sai da ya gama bin kowa da kallo, daga inda yake tsugune gaban mahaifiyarsa ya yi masu gaisuwar jimula ta hanyar fadin" Sanunku dai" Kanwar mahaifinsa ce ta tabe baki tana dauke kanta a ranta tana ayana' Haka fa, dan so wanda aka daurewa, ana iya zagin namu ya'yan tassss ama banda shi, in iskancin ne da rashin mutuncin ya dame kowa, nan dan rashin da'a har ware kansa ya yi daga cikin familly ama kuma a haka ake masa tarbar da ta fi kowace mutunci a cikin ya'ya, ba damuwa shi din da ake so sai ya kawo abin kunya a wannan ahali da izinin mai sama!' Sai dai du bacin ranta ba zai fito fili ba, bakinsa a zuciyarta, dan HAJIA dake wajen, dan du abinda za'a fada banda zaginsa a gabanta, basa shan inuwa daya da junna ama kuma kowa ya san tana shayinsa "YUSUFA, gaisuwar Kennan ?" HAJIA ta fada, da muryarta mai dauke da tsufa da alamun rashin lafiya Sarai ya ji ta, ama ya yi tamkar baya wajen, har sai da suka ringa mintsininsa bibiyu mahaifiyarsa da mahaifinsa sannan ya yi dan murmushi ya kallo wajen da RISLAN ke masa alamun ya gaisheta mana, ga janwar RISLAN din tunda ya zo kanta ke sade tana wasa da yan yatsunta zuciyyarta na dokawa da rigimar da take son rajabowa kanta Kansa ya cire ya maida kan hajiar, kamar daga sama ya ce" Sanu fa" Sai kuma ya daure fuska yana dauke kansa Sai da HAJIA ta sauke ajiyar zuciya na bacin rai tana kallonsa ta ce" Shikenan gaisuwar? Shin baka ji na karye ba? Ko baka ji ba da ka shigo yanzu ai ka gani ko? Ama maimakun ka min gaisuwar da ta dace da tausayawa sai kace da Ni sannu? Haba YUSUFA " "Haba HAJIA, haba HAJIA, wai kar ya gaishe kin mana, dan Allah kar ka gaisheta Yusuf sai me? In ba dan sarkafa irin ta HAJIA ba yaya za'a yi uwarsa ta ki ki shi ya so ki? Ba zai taba sonki ba HAJIA ko me zai same ki ya same ki ba damuwarsa bace, to wai da wane zai ji ne? Mutumen dake fama a gidan giya da kuma bin mata yaushe yake da tunanin tausayin wani nasa ko jin kai?" Kanwar mahaifinsa ke fada da yannayin hayaniyar da ta dan lafa bayan shigowarsa Mahaifinsa me ya fara maganar shima ransa bace ya ce" A'isha kar ki saka mahaifiyarsa a ciki, yaro ne ka haife shi baka haifi halinsa ba, da ace halayar mahaifiyarsa ya yi da mun ji dadi, ama yaron nan sam baya jin magana, ba sai kin hada da mahaifiyarsa ba, bata da laifi a halayarsa, itama babu yadda zata yi da shi ne, giya kuwa da mata ai su ya ba gaba sai hakuri" Kansa ya sake sadawa sakamakon matse hannunsa da mamansa ta yi HAJIA itama ta budi baki rai bace ta ce" Kin cuceni Balaraba, ban san me na maki da zafi ba, kin yi tsaye tsayin daka kin hadasa gaba da jikana, Ni da ke sai dai Allah ya saka min dan ba zan taba yafe maki ba, domin inada iko a kan yaron nan kuma Allah ya sani!" "Dan Allah ku yi hakuri" RISLAN ya fada a sanyaye yana jin zuciyarsa na karyewa, da yake da fashewa da kuka kamar yadda kanwarsa ta fashe da shi dan ana zagin Yusuf , dan sauran ya'yan tunda ya shigo suka fece, itama tana zaune ne saboda Mamanta na wajen, bata san haka zata faru ba da bata zauna ba, shin yaya zata yi da ranta a kan kiyayar da mahaifiyarta ke yiwa Yusuf?, Mamanta na masa kiyaya wace ta kazanta ita gashi Allah ya jarabeta da jarabtar dake neman halaka tunaninta, a Tata kadarar rayuwar tana ji a ranta koda makashi ne Yusuf tana so, ko menene hakayansa ta ji ta gani zata iya rayuwa da shi a haka, dama tana daya daga cikin masu masa yaki a gidan nan, ko yanzu itace ta tunawa kakarsu baya so fa yana waje kishiyoyin mamansa na nan ai kuwa kakar tasu ta salami kowa sai su ya su, gashi su dinma sunna neman daga masa hankali, dan a yadda kansa ke sade daga inda take tana gannin tarin zufar dake taruwa a goshinsa Itama muryarta a sanyaye sosai ta ce" Mama dan Allah ki yi hakuri ki bar yiwa Yaya biya maradi haka" Idannuwansa da suka kada suka yi ja ya dago a karro na biyu ya zubawa mahaifinsa su, sai kuma ya dauke ya sake duban mamansa wace kanta ke kasa ba zaka iya gane hallin da zuciyyarta ke ciki ba Hannayenta dake kafadarsa ya kamo a hankali ya dan murza sannan ya mike daga gabanta ya maida hularsa saman kansa ya juya da nufin tafiyarsa HAJIA ce muryarta na rawa ta ce" Tafia zaka yi ko kallona ba zaka yi ba?" HAJIA A'isha ta ce" HAJIA dan Allah ki koyi hakuri da shi, tunda ya nuna maki baya sonki ki yi hakuri mana, Allah ya sa ba shi kadai kika malaka ba bale ki yi kukan rashin jika, ita uwar tasa ya jika ya sha ta iya masa komai in an isa" "Haba aunty....." Yusuf ya fada a hankali yana sauke mata kaifafun idannuwansa a saman fuskarta tar da tar A hankali ya dauke ya sauke saman fuskar RISLAN da ya sada kansa saboda jin nauyin dan uwansa, wanda suke kaunar junnansu ama a kulun iyayensu na kokarin hadasa fitina a tsakaninsu, sam mahaifiyarsa bata son tarensu A tausashen da sosai mahaifiyarsa ta yi mamakin ganninsa a haka ya ce" Ka gani? Sai da nace maka ba zan zo ba, ka nuna min ikon da kake da shi na iya tankwasani ka sakani zuwa wajen da ake kallon idannuwa a wulakanta min mahaifiyata sannan a kirayeni mashayi mazinaci bayan mawakin kansa ya boye nasa kirarin?, RISLAN ka fadawa mahaifiyarka ana dane wasu abubuwan saboda albarkacin albarkaci, dan Allah ta rufa mini asiri kar tarin sunayen lalatacen dake kaina su karu ace bayan shaye shaye da zinar kuma na kara wasu, dan ina mai tabbatar maka irin yadda take jin mahaifiyarta Ni na fita ji, domin Ni ba zan kasance kananzir din daga hankalin uwata ba, har abada, abinda ya sa zan bar nan ba tare da na karya yatsar da aka nuna mata ba, kuma ka yi hakuri ka daina zuwa inda nake na roke ka!" Daga haka ya fice ya mako masu kyauran kofar da ya yi wani irin karan gaske sannan ya nufi wajen motarsa ransa a bace ya bude ya shiga ya ga babu yan matan sai ishak da direba kadai, dan tunda ishak ya ga ya shiga ciki ya salami yan matan nan dan ya san yau ba show sai masifa Bayan tafiyarsa shiru ne ya fara zagaye dakin baki daya kafin HAJIA A'isha ta shiga share hawaye kamar yadda ta saba ta ce" Shin yaya zai iya karbar mulkin garin nan? Shin me yake yawo a cikin gidanmu wanda YUSUF ke son falasamu ? Du fadi tashin da ake yi da sauki tunda bai fita waje ba, gashi yana so sai duniya ta san me muke ciki?, Yusuf sai kace annoba a cikin wannan ahali!" Da sauri Anna ta zubawa HAJIA A'isha ido, zuciyyarta na tafasa sosai da magangannunta Ya Allah, shin basu san karra bane mutanen nan ko ake yi ta yi wani motsin da za'a ce ta yi ba daidai ba? Kai ta sake sokewa tana ta hailala da ambaton sunnan Ubangijinta, dan tana so ne har su yi su gama bata tanka su ba, sannan tana nemawa danta tsari daga furucin bakunnansu Mahaifinsa ne ya dauki magana cikin yannayin da ya riga ya zama jikinsa rayuwar yau da gobe yana fadin" Asalamu alaikum jama'a....mun zo maku da nagartacen ingantaccen maganin Ulcer, magani ne na Hausa jikake wanda Dubai suka gwada suka ji dadinsa, nagartatun tsatatatun itaciyoyin da suka bamu sasake masu anfani ne ake anfani da su, a nan jamhuriyar Nijar a garin Damagaran a farashi mai rahusa dubu biyu yan naija , yan nijer kuwa 1500francs mai bukata ga numbar +227 96897192 , HAJIA RAHAMA 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *AZAL!* 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *SAJIDA NIJAR* *PAID BOOK* _Bismillahir rahamanir-rahim._ *6* *wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nigar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍* *TALLAH, TALLAH, TALKAH* _*TOH TO TO!*_ 🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_ _Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_ Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake _Amarya_Uwar gida_ _Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_ _Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_ INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼 🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI* *🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU* _KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_ _SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_ 💁🏽‍♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻* 💁🏽‍♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI… _MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_ *ADRESSE 94536935 94.53.69.35* *Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER* KARKU BARI A BAKU LABARI🥳 Litattafan marubuciyar Duk karyar kada Yar mahaukaciya Bak'a ce Bani da zabi Daga tafia daukar soja Neman na kaina Kutkale Mage Bani da zabi Idan ka raina inda kake Umughuluk itifal Duk nisan jifa Wata kokowar Ni zan ladabi Dakika biyar Da ciwo a zuciyata Aure yakin mata Alkalamin Kadarata Dutse Daga tafiya daukar soja Makauniyace ND now *AZAL* Mahaifinsa ne ya dauki magana yana fadin" Wace sarautar? Shima ai ya fito fili ya nuna bata gabansa, kema kin san a matsayin da ya taka a yanzu babu mai tankwasa shi amsar sarautar kauye, Bama zai yarda bane da wannan maganar, Ni ba abinda ya fi daga min hankali irin yadda HAJIA ke saka shi a ranta, ba zata iya hakura da shi bane ko menene oho, tunda ya nuna baya son zama a nan din ai sai a hakura" HAJIA dake fama da kanta ga kuma abinda ya faru ido rufe ta shiga fada tana fadin" Ni dai abinda kuke min bana so, a kulun fada maku nake yi a kan yaron nan ina iya BATAWA kowa, yanzu da baku masa haka ba ai da bai yi fushi ya tafi na, rabona da shi a kadan an kusa wata biyu, yau dalili ta yi ya zo inda nake kun harzuka shi, Ni bana gannin laifin jikana, na uwarsa nake gani, itace ta bude min hanyar komai ta halayarsa, ta Saïda gadonta ta masa jari bayan ita ta san mu ba matsiyata bane, ta saka du ya tsani kowa sai ita kawai yake so, ba damuwa Allah sai ya saka min ku tashi ku bar min waje Ni na ji da abinda yake damuna!" Anna ce ta fara sauke ajiyar zuciya ta ciciba ta mike da kyar sannan ta karasa daf da HAJIA ta duka a tausashe ta ce" Allah ya bada lafiya HAJIA, Allah ya huci zuciyarki" HAJIA ta kawar da kanta bata amsata ba har ta mike ta fice daga dakin gaba daya tana tafiya a Nutse ta nufi hanyar ficewa a kafarta du irin daren da ya tsala Kasancewar mahaifin Yusuf bai fito da wuri ba sai da ya salami sauran matansa ya je ya yiwa ɗan uwansa salama wanda shine sarki a yanzu sannan ya fito ya nufi motar yana Adu'ar Allah ya sa ta kunna AC kar aje haka ta zauna ita da bata son zafi Yana karasowa ya ga motar wayam babu ita a ciki gabansa ya yanke ya fadi Da sauri ya sake dubawa ya ga eh lalle fa bata cikin, hakan ya sa da sauri ya shiga nemanta a farfajiyar gidan dan ya san da wahala ta koma cikin gidan wajen kowa dan kusan tsanar da HAJIA ta yi mata ya sa bata shiri da kowa, kowa ya tsaneta a gidan sai shi da yake son abarsa tamkar ransa Yana son mahaifiyar Yusuf fiye da tunanin bawa Ciwon ta bai taba damunsa ba Bai taba gajiya da tatalinta ba Duk irin tsakaninsa da mahaifiyarsa ta gaza sakawa ya saki Mahaifiyar Yusuf wace take ikirarin nauyi ce a wuyansa marar anfani, bata da wani anfani a duniya sai na karar da dukiyar yaronta, kulun ita ba lafiya kulun ana hanyar fita da ita neman lafiya, babu irin matsin da bata masu ba dan mahaifiyar Yusuf ta fita daga ahalinsu da kaffafuwanta ama ta jure ta kawar da kai take zaune a gidan ba dan komai ba sai dan yaronta daya jal dake rayuwa cikin gararin yau da gobe da yan uba gaba da baya, wanda abin ya shafo harda Mahaifinsa domin yau da gobe ta saka abinda kanwarsa da wasu ke fada masa a kan yaron nasa shima ya fara kwaikwayar yarensu yana fadin abinda ba ALKHAIRI babu kuma magani ma yaron nasu, tana zaune a wannan ahali ne dan ta sani komai tsiya adu'arta itace a sama da ta kowa dan haifa ta yi, kuma ita ta sani koda kare da sata dadawa da warinta, Allah ya kadarta mata aure a irin wannan ahali bata da yadda ta iya sai hamdallah da neman hanyar gannin shiryuwar yaronta dan babu abinda ya gagari Allah, kuma ko wa zai zagar mata ba zata rama ba, zata fadawa Allah ya isar mata ta hanyar shiryar nata gudan jinninta mai sonta da kiyaye bacin ranta, to in bandama abin fada da baya masu kadan yau har sunna da bakin gorantawa wani abubuwan rashin ji na yau da kullum? To wane ba wane ba makaho a bisa makahon doki! Kiyaya ce an dasa a zuciyar mahaifiyar mijinta Tata tun kafin ta shigo gidansu, an fadawa mamansa cewar idan ta yarda aka auro irinta to fa zata rabata da danta, sai aka yi rashin dace dan nata na yiwa maman Yusuf makahon so din da cece kuce din mutane suka yi tasiri a zuciyyarta, tun ana boyayiyar kiyaya da shayi har aka dawo yau da gobe da zama waje daya ya sa ake abu kamar a zamanin jahiliyya, sai dai basu sani ba, ciwon da take fama da shi na gwuiyoyi bai taba kwakwaluwarta ba, hakurinta kuwa ta jima da YANKEWA kanta zata ci gaba da yinsa ne da mahaifiyar mijinta kadai, itama dan tana yar halak, duka sauran zata basu amsoshin tambayarsu a daidai lokacin da ya dace Nemanta yake yi hankalinsa tashe har bangaren HAJIA, inda ta ja tsaki rai bace ta ce" Ni kam yau na hadu da balakin wannan mata, to yarinya karama ce da zaka wani daga hankali dan baka ganta ba? Allah ya sa Allah ne ya rabaka da kaya!" Jiki a sanyaye ya fito daga ɓangaren hajiar ya nufi motarsa ya tayar yana tambayar masu tsaron fadar a zuciyarsa yana tunanin ina ta nufa duba da yar tafiya tsakanin fadar da cikin baban gari Damagaran, inda gidanta yake, gashi dare ya yi kuma Yusuf ya jima da tafia Sosai kirjinsa ke dokawa, hankalinsa gaba daya ba a jikinsa ba har ya samu ya karasa gidansa Tun daga bakin kofa masu gadi suka sanar da shi HAJIA ta dawo hakan ya saka shi sauke wata irin ajiyar zuciya sannan ya karasa wajen ajiyar motoci ya parker watsetsiyar motar da YUSUF ne ya cenza masa ita cikin sababin da suka shigo ne sai da mahaifinsa ya fara murzarta kafin ya sake su kasuwa A sukwane ya karasa baban falonta yana ambaton sunnanta Shirun da ya ji ya tabbatar masa bata nan dan haka ya nufi karamin falonta na cen cikin dakinta Zaune ya sameta saman kujera waya a kunnenta tana magana a hankali, wanda ya tabbata da Yusuf take maganar dan idan ka ga ta maida hankali tana magana cikin nutsuwa da tausasawa sosai da yaronta take magana shi kuwa yana zuba mata rigima A tausashe ta ce" Ka tabbata ka daina fushin? Idan baka daina ba nima fushi zan yi fa?" Yusuf ya saki dan murmushi yana jin nutsuwa na shiga dukan gaban jikinsa, shin yaya suke tunanin zai iya gannin darajar duk wani mai son wulakanta masa ita? Idan ya rasata a duniya shi ya san ya gama lalacewa, ko a yanzu ya san cewa adu'arta ke tafe da shi ba komai ba A Nutse ya ce" Na hakura Anna, ina gidana yanzu haka" "Allah ya maka albarka ya tashemu lafiya" Da kula da tarin kauna ya amsa ya katse kiran har yana sauke ajiyar zuciya ya lumshe idannuwansa yana jin ciwon irin yadda ake saka masa uwa a gaba a wulakanta saboda shi A hankali mahaifinsa ya karaso inda take zaune ya zauna ya mika hannu ya riko lalausan hannunta yana kallonta ya ce" Me yasa kika tafi kika bar ni? Wa ya kawo ki? Kin san irin yadda hankalina ya tashi kuwa?" A hankali ta janye hannunta daga cikin nasa tana kallonsa ido cikin ido a tausashe ba da rigimar komai ba ta ce" Aban Yusuf, me yasa tsanarka a kan yaron nan ke hauhawa a kulun ne?" Dan tsai ya yi yana kallonta , a hankali ya koma ya gyara zamansa cikin kujerar still yana kallonta gannin amsarsa take jira Da kula sosai ya ce" Ban tsane shi ba, ke kin san shi din shine mafi soyuwa a zuciyata a cikin yayana, ina yi masa haka ne dan ya ji haushi ya daina abinda yake yi, me amfanin kana aikata laifi kuma kana yi a idon kowa? Ai ko Allah ya Hanna ka ringa tonawa kanka asiri, gashi baya son danginsa, ban san me suka yi masa ba baya son su, ace du irin yadda HAJIA take da shakuwa da shi ba zai iya sonta ba? A kansa kadai HAJIA ke yin kuka a duniya ama fir ya kasa ganewa ya rabeta ko dan tsufanta?" Kai HAJIA AMEERAh ta cire daga duban gefe ta maido kansa tana dubansa, a Nutse ta saki dan murmushi a tausashenta ta ce" Ka yi hakuri ka ringa duba furucinka a kansa, saboda mahaifi kake a wajensa , ko me yake aikatawa fatan shiriya shine ya dace ya fito daga harshenka, ka yi hakuri ka fi karfin zuciyarka domin baka sani ba abin ya fara fin karfin son ka ga ya dawo hanya ya koma abin birgewa wa zuciyarka yin daidaya da zuciyarsa" A hankali ta ajiye maganar kafin ta dago ta saka idannuwanta tar cikin nasa ta ce" Me kake jira daga wajensa ? Ina ganin shi yana sara da duban bakin Gatari , da ace irin halayan da ake masa zai yi da an shiga uku, shin wani d'a za'a zagi mamansa yana tsaye bai dauki mataki ba? Fin karfin sa na yi shi yasa shi kuwa ya kaurace dan kar ya aikata aikin da za'a Dube shi da shi, me yasa bakwa masa adalci ne? Me yasa bakwa dora abinda yake iya ji a zuciyarsa kamar yadda kuke iya ji? , me yasa kuke gagawar yanke masa hukunci idan ya wulga koda bai yi tari ba?" Wannan karronma a hankalin ta ajiye maganarta sai dai dubanta na iya fasara daf take da tsinkewa A Nutse ta dora da fadi " Yau da gobe nake guje maku, dan ba zan ware kowa ba, idan Ni na zamo takalmin takawarku shi a abu mafi daraja yake kallona, in ma me na aikatawa ahalinku wanda kai ake iya yafe maka Ni ake kallona a matsayin *AZAL* din da ta afko ahalinku da cikin da na ba kaina wace ba za'a iya hakuri a Dube Ni ba, shi yana dubana a mutun mafi daraja a duniyarsa, shin yaya kuke so yaron da kuke kiran uwarsa masifa shi ya zamo maku mai biyayya a gabansa? To ai koda ace shine shegen da muka yi Ni da kai ba zai taba fa......." "AMEERAH!" Hon Bello Muctar Gali ya fada yana dagowa daga jinginar da ya yi hankalinsa na neman tashi zuciyarsa na bugawa, domin tunda suke da ita du irin abinda yake faruwa bata taɓa dubansa ta nuna bacin ranta ba, kai komai bata fadi bale har ta tado abinda shi ya birne yake kuma zaune da matarsa da zuciya daya da so da kauna Duda ita ya san ba lallai in ta iya manta baban abin da ya shiga tsakaninsu a zamanin samartaka ba, sai dai ga dukkan alamu abin na ranta har yau kunnayensa ke jiyo masa maganar dake daf da dauke nutsuwarsa A hankali ta zuba masa ido kafin ta tari numfashinsa tana dan Bude lumsasun idannuwan da yaronta ya yi gado a wajenta tana kallonsa ido cikin ido a kausashe sosai ta ce " BELLO, idan maye ya manta uwar d'a ba zai yiwu ta manta ba, yayana da aka ciro a dakin tiyata aka nunan sun mutu ba zasu taba guguwa a zuciyata ba, ba zan taba mantawa ba!" Sai kuma ta sasauta muryarta tana jingunuwa da jikin kujerar nan a hankali ta ce" Ina daukan zamana a ahali irin naku matsayin jarabawata ina kuma rokon Allah ya zamo silar yafewar laifin da na aikata, sai dai ka sani ina guje masu yau da gobe a kan D'ANA!, i love my love fiye da raina, ku kun san biyayar aure da shi ke rikeni ba dan bani da yadda zan yi ba!, Ni ce AMEERAH (GIMBIYA) ta DAMAGARAM, banbancin mai nisa ne!" Daga nan ta yi shiru tana jin kanta na neman yi mata ciwo Hon Bello kuwa sai ya rasa shin mamakinta yake ciki ko firgicin halin da take ciki? Lalle a yau an kaita bango, ashe itama tana iya nuna bacin rai a kan abinda ake yiwa Yusuf har haka? Ajiyar zuciya ya sauke a sanyaye ya mike dan ya dauko mata maganinta da ya zamo kulun sai ta sha take kwonciya Sai da ya je ya dauko ya kawo ama fir tace ba zata sha ba, wannan shi ya karra daga masa hankali domin idan ta yi fashin sha da wahala in bata KWONTA rashin lafiya ba, a hankali ya so sake fahimtar da ita ba zai taba iya kin gudan jinninsu ba, ama akace ka guji fushin wanda baya gagawar fushi, cikin wani bacin ran kafin ta mike ta nufi dakinta ta ce" Ka shiga tsakanina da A'isha!, ta fita a hanyata, abinda na hadiye na shekarun baya ba zan iya hadiyewa yanzu ba, kanwa take a wajenka , koda yaya ce ina iya dakatar da ita bale kanwa, ta guji budar bakina dan idan ta kirayi YUSUF mazinaci mashayi bata san me zan kirayi nata ya'yan ba wa'inda ba hasashe nake yi ba ko Kazafi, tana yawan kirana *AZAL!* idan aka bibiyi tarihi kalmar AZAL ta yiwa ahalinta kadan , a kan YUSUF babu abinda ba zan yi ba ciki harda rabuwa da UBANSA!" Daga nan ta yi dakinta ta rufo ta saka ky ta murza da karfi sannan ta karasa wajen gadonta tana rike kanta ta KWONTA jiri na neman summar da ita daga kwoncenma A falo kuwa da kyar Mahaifin Yusuf ya iya samun waje ya zauna yana dafe kansa da hannayensa bibiyu A hankali ya bude idannuwansa sakamakon tuno ranar da yayansa ya fito da wani zannin gado a hannunsa rungume da jajirai biyu farare sal masu kama da shi tak tak Duda jajirtakarsu kamar ya yi kaki ya tofar kamanin har sun bace ko dan Allah ya nuna masu cewar ba gardama abinda suke gudu nasu ne? Yan jarirai sun yi fari fat na alamun ba rai a tare da su ya nuna masa, bai ko bashi damar runguma ba ya fice da su yana fadin abinda aka tsara za'a sanarwa duniya cewar ba kumburin cikin haihuwa bane ta yi dawainiya da shi, kumburi ne na kari dake girma tamkar cikin haihuwa yana ji yana gani bai san inda aka birne masa yayansa ba, haka uwarsu ko ganninsu bata yi ba aka yi rufa rufa ga zafin haihuwa na cs ga radadin rashin ƴaƴanta aka dawo gida aka daura masu aure a ranar tare da wasu matan biyu, wa'inda HAJIA ta zaba masa yana ji yana gani bashi da ikon furta ko kalma daya kuma aka nuna aurenta shine karshen daurawa kai fin karfi dai aka nuna ba zata tare a gidanta ba a kalla ta kusan shekarewa a tare da HAJIA , galazawa babu irin wace bata gani da Hajiar da kanwarsa A'isha, yayansa kuwa dama basa ko ga maciji da ita, shi dai bai nuna mata tsana ba ama kuma bai nuna mata kauna ba, a wajen su HAJIA kuwa nan ta ringa tsintar sababin sunnaye masu girgiza zuciya, gashi a lokacin ba damar ta je wajen Tata mahaifiyar saboda ta yi fushi da ita sosai, sai a rasuwar mahaifinta suka amsheta suka yafe mata har suka janyota jikinsu, ama Duda haka babu ruwansu da damuwar dake damunta na dakin mijin da a ganninsu ba gidan aurenta bane, gida ne mai hatsarin gaske , gida ne da jita jitar da ake yadawa a kansa ya sa da yawa ke masa wata irin fasara, su tasu sarautar mai hatsarin da baki ba zai iya misaltashi bane, wani abin ne a bine a ahalinsu ya sa haka ko Allah ne ya kadarto masu haka a rayuwarsu? Allah shine masani, ama yannayin matarsa na yau ya girgiza shi fiye da tunanin bawa Menene bata gani ba? Bata taba nuna masa ba Idan yana fada ma Yusuf takan kauda kai ta yi murmushi ne ta ce" Sai addu'a Aban Yusuf" Ama a yau ta fadi abinda yake gannin shi dai bata yi masa adalci ba Shin yaya take tunanin zata haifo masa d'a tsatsonsa ya tsana? Yau ko ba nasa bane in dai daga jikinta ya fito ba zai taba tsanarsa ba, bale nasa ya Allah yaya zai iya tankwasa zuciyar wace bata cika fushi ba?....... 🤔🤔🤔🤔🤔🤔🤔 Asalamu alaikum jama'a....mun zo maku da nagartacen ingantaccen maganin Ulcer, magani ne na Hausa jikake wanda Dubai suka gwada suka ji dadinsa, nagartatun tsatatatun itaciyoyin da suka bamu sasake masu anfani ne ake anfani da su, a nan jamhuriyar Nijar a garin Damagaran a farashi mai rahusa dubu biyu yan naija , yan nijer kuwa 1500francs mai bukata ga numbar +227 96897192 , HAJIA RAHAMA 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *AZAL!* 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *SAJIDA NIJAR* *PAID BOOK* _Bismillahir rahamanir-rahim._ *7* *wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nigar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍* *TALLAH, TALLAH, TALKAH* _*TOH TO TO!*_ 🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_ _Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_ Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake _Amarya_Uwar gida_ _Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_ _Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_ INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼 🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI* *🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU* _KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_ _SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_ 💁🏽‍♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻* 💁🏽‍♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI… _MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_ *ADRESSE 94536935 94.53.69.35* *Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER* KARKU BARI A BAKU LABARI🥳 Litattafan marubuciyar Duk karyar kada Yar mahaukaciya Bak'a ce Bani da zabi Daga tafia daukar soja Neman na kaina Kutkale Mage Bani da zabi Idan ka raina inda kake Umughuluk itifal Duk nisan jifa Wata kokowar Ni zan ladabi Dakika biyar Da ciwo a zuciyata Aure yakin mata Alkalamin Kadarata Dutse Daga tafiya daukar soja Makauniyace ND now *AZAL* A gidan su RAUDA Tun karfe shida na safe hayaniya ta kaure a tsakar gidan, wace ta hannata mikewa bale ta je ta samu ta dauro alwallah ta gabatar da sallar asubahi, rikici ne wanda yake tashi sama sama, fada ne irin na matar mashayi da mashayi, fadan da farkonsa aka sani ba'a san karshensa ba, fadan da du tsiya da zarar ya nuna zai rabu da ita take komawa ta yi mikis kamar ba ita ba, du gorin da take yi, du masifar da take yi cewar an hadata da balaki an aurota ba'a ciyar da ita, ba'a shayar da ita, an kawo mata rikon ya'ya an zuba mata irin tsiya gayar tsiya ba zata iya ba fatanta Allah ya rabata da masifa da BALAKI, domin auren Umar masifa ne da BALAKI ba komi na, ba karuwa sai raguwa , babu farin ciki sai bakin cikin rayuwa, na kulun hauhawa yake yi ba raguwa ba, da zarar ya nuna wai su saki hannun junna mana sai ta shige daki ya labe ba zaka kuma jinta ba sai ya fita ta fito ta wulakanci su RAUDA da dan uwanta wanda tsoron maman nasu ya saka ko muryarta ya ji sai jikinsa ya kama rawa ya shiga neman wajen buya Ido Rauda ta rintse sakamakon wata ashariya da Mama ta kyatsa tana fadin" WALAHI baka isa ba, baka isa ba Umaru, kudin da nake binka ai sun fi haka, a kan me zaka ce zaka siyawa RAUDA kayan makaranta da kudina? Kar ta yi karatun mana, karatun nata da ba anfanar uban kowa zai yi ba, yawon banzan da take fita ne kake kira karatu ko me kake so ka daukeni? Yau da ace wannan yarinyar ba y'ar zumunka bace har na yi maka wata fasarar, ama Duda haka zan zuba ido sosai dan WALAHI karya ne ba'a yi y'ar da zan gogi arzunzumi ta goga ba.... ba z........." Wani irin karan duka da ya shiga kunnayensu ya saka su duka biyun rintse idannuwa, hawayen da RAUDA ke rikewa suka samu damar fita da gurbin idannuwanta shar masu zafi da radadi, shi kuwa kannin nata ya rarafa ya boye a jikinta jikinsa na rawa kirjinsa na dokawa kamar zai summa Ihun kukan Mama da y'arta ke tashi sama sama tana fadin " Allah ya isa tsakanina da kai, dan na fadi gaskiya zaka dakeni? Menene ba'a yi a duniya yanzu? Ni dai da RAUDA da iyayenta sai Allah ya mana hisabi, tunda suka fadi suka mutu ka zama mashayi ka kawo min ƙatuwar budurwa ka saka min ga wani dama da nake riko, ba zan yafe masu ba kuma kaima ba zan yafe maka ba dukana da ka yi, kuma na fada sai na saka ido a kanku dan ban yarda da mashayi ba, in kuka sha kun san abinda kuke yi ne? Ba zan kyaleka ka wulakantani ba Umaru!" Shi din da kansa a tsayen da yake yana haki zuciyarsa tamkar zata balo kirjinsa ta fito hawayen ke wanke masa fuskarsa Gannin idan ya zauna yana iya kasheta ya saka kansa a uku ya saka ya juya kansa na sarawa ya nufi hanyar fita A lokacin da ya fito waje idannuwansa suka sauka a kan makocinsa da kuma limamin anguwarsu sunna tsaye daga nesa da gidan kadan ama ga dukkan alamun gidan hankalinsu yake Yana yin ido hudu da su kunya da tsananin takaicin kansa suka rufe shi, a hankali ya dakata ya so juyawa sai dai makocinsa ya ki bashi wannan damar ya karaso inda yake tsaye ya mika masa hannu yana masa Salama Hannun nasa ya kalla, sai ya ringa jin dari darin bashi nasa dan na makocin nasa a wanke tasss ga tabjinsa a hannunsa yana ja har wani kanshi yake, shi kuwa nasa harta miyar da ya ci jiya da dare bai wanke ba, sai kunya ta saka shi kallon nasa hannun ya nemi nokewa Karasowar liman ya riko hannun nasa suka yi musabahar dole yana kallonsa shima a tausashe ya ce" Shin ka yi sallar asubahi?" Wata kunyar ce ta sake kama shi, to rabonsa da yin Sallar asubah a kan lokaci ai har ya manta, dan haka ya sada kai yana cike da jin da kunya Ajiyar zuciya liman din ya sauke a tausashe ya ce" Mu je ka gabatar da sallah, itace abinda take gaba da komai a yanzu, bismillah" Kamar kanninsu ko dan gidansu suka saka shi gaba, ba da niyar tozarci ba, a'a da niyar taimakonsa, dan kuwa kasancewarsa mutum dake rayuwa cikin halin maye bai Hanna masa girmama duk wani mutumen Anguwar ba, datijawan Anguwar na binsa da Adu'ar shiriya, da kuma fatan Allah ya shiryi matarsa, dan babu wanda bai san wacece ita ba, dabi'unta a bayyane suke ba a boye ba, irin yadda take yiwa Rauda kuwa da kanninta ya zamo kowa na yi mata wani kallo, gashi dai kiri kiri tana son mayar da yarinyar kamar wata mai zaman kanta, a koda yaushe cikin zance da masu motoci a kofar gida, a koda yaushe tana karbar baki a kofar gida Makocinsa na hannun dama ne da liman din suka zauna sai da ya gabatar da sallar asubahi har karfe bakwai na safiya ta gota sannan suka zauna tare da shi, cikin nutsuwa da kula suka ringa yi masa nasiha da nuna masa irin illar wannan rayuwar, abinda ya riga da ya sani, ya kasa zaunawa ya yiwa kansa fada ne saboda bashi da mai tunatar da shi A tausashe Liman ya ce" 300Babu yadda rayuwa bata zuwarwa bawa, kuma komai girman laifinka idan ka tuba Allah mai karbar tuban bawansa ne, babu abu mafi hatsari irin maye, maye bashi da anfani Malan Umar, mai yin maye bashi da daraja kuma bai san abinda yake yi ba , kana da ya'ya yan mata, ga namiji masu bukatar taimakonka, dan Allah ka ceci kanka ka daina wannan halaya, ka rufawa kanka asiri kar ka samu matsala a wajen aikinka, domin rayuwa yau kana gannin idan mutun bashi da aikin yi damuwa ce, gashi kai din nan uba ne kuma Magidanci ne malam Umar" Makocinsa Elhaji ashiru, mutun ne mai abin hannunsa daidai gwargwado kuma mai kyauta da taimako, ya jima yana da burin gannin sun samu kusanci da makocin nasa dake gaishe shi idan ya ganshi ko a ina ne Allah bai yi ba sai yau, ya Dube shi da kula sosai ya ce" Kowani bawa da irin tasa jarabawar makan Umar, kuma kowa lalube yake yi , babu abin tsoratarwa da wannan duniyar sai irin yadda babu wanda ya san ranar mutuwarsa, idanma babu mutuwa malam Umar Akoy tsufa wanda ke yiwa mutuwa fadan garaje gareta ta bar bawa da shi ta gani, malam Umar duniyar nan mutun ya yiwa kansa abin kirkima yaya ya kareta bale yana wasa da damar da Allah ya bashi? Bama kamar sallah da kiyaye hakokin ubangiji, ga nauyi a wuyanka a rataye, kaine uba kuma uwar ya'yan nan, ka yi kokari ka fi karfin zuciyarka ka fuskanci rayuwarka ka daidaita abinda ya dace ka daidaita, idan kana bukatar taimako ko na menene ka same ni in sha Allah Ni zan kawo dukkan talafin da ya dace, kana da halaya masu kyau, domin kaf Anguwar nan babu wanda zai ce ga abokin gabarka ko wani abin ya haɗaka da wani saboda dukiya ko ya'ya, hakan kuwa baban ALKHAIRI ne shi yasa yanzu na zo shiga gidana daga masallaci na ringa jin hayaniyar nan na kasa hakura na tabo liman muka yi jiranka, ba dan mun saka maka ido a shige da ficen gidanka bane, a'a, damuwa muka yi da dan uwanmu musulmi muka kasa hakura sai mun sauke nauyin hakin makotaka " Sosai uncle din Rauda ya karra jin zuciyarsa ta yi sanyi, hakan ya sa shima ya gyara zamansa yana sauraron nasiharsu da kuma tunatarwa a kan gobe kiyama da kiyamarsa, ya shiga halin tunanin idan mai kasancewa ta same shi a irin wannan halin? Me zai cewa ubangijinsa? Tsoro ya kama shi ainun hakan ya sa ya zauna tare da su sunna ta zamtawa A cikin gida bai san ya fita ya balowa RAUDA gagarumin rikici bane A lokacin da ya fita Mama ta gama kukanta ta mike ta nufi dakin su RAUDA ta bankada kasarin dake kofar dakin ta shiga rai bace ta mika mata hannu ta ce" Bani!" Gaban Rauda ya yanke ya fadi, dama ta san a rina wai an ari zanin mahaukaciya A hankali bayan ta sake riƙe hannun kanninta dake ta rawa ta ce" Mama jiyan dare na yi gudun kar ya min shi yasa na dawo gida dan kar na yi dare ki kasa barci ba'a rufe gida ba" Sai da maman ta dan kankance ido tana kallonta kafin ta shigo gaba dayanta ta ja yar kujerar tayani tsegumin da ita ta sanyota dakin ta zauna tana kallon Rauda ta ce" Ama ban taba gannin yar bakin ciki, marar mutunci irinki ba, ban taba gannin munafuka algunguma irinki ba, dan ubanki na taba zaman jiranki idan kika fita ne? Nan ko zance kike yi sai ki kai karfe goma sha biyu na dare a waje kina yi na taba zaman jiranki ne? Ko saurareni da kyau na rantse Miki karya kike yi, kin ga a yau idan har baki bani abin kirki ba sai na maku horon yinwa ta wata guda cir kuma sai kun bar min gidana , tunda kin san ba ubanku ke biyan haya ba, ke in banda raini da wulakanci da bakin ciki har nice zaki kawowa wannan maganar? Ai ba ubanki ya kawoni duniya ya tafi ya barni da wahala ba bale na zauna ina ciyar da gandamemiyar kamarki a banza ba, na fada maki kirarki ta ki nemo min kudi ce, ba ruwana da wa ta yaya! Matsalata kudi, idan kuwa tsiyar da iyayenki suka mutu cikinta zaki nuna min ba matsala, dama ke kin san har ki mutu ba zaki mallaki abin kanki ba, ama Ni WALAHI sai kin nemo min in ba haka ba......." Da karfi ta janyo Abdul Hakim ta rike hannayensa ta kashe shi da marin da ya saka RAUDA saurin mikewa ta janye shi jikinta na rawa ta kafe fuskar Mama da kallo Maman kuwa ta mike tana kallonta itama ta ce" Dukana zaki yi yar mararsa mutunci? To WALAHI na fada maki idan baki nemo min kudi ba sai na halaka wannan kafin na halaka uban baki kema na halaka ki, ba kin fada min saboda su nake taka ko ba? Zan ci gaba da taka ki ko bayan na halaka su in dai kika yarda kika yi wasa da umarnina y'ar matsiyata mai shegun idannu kawai, ki miko min shi ya je ya kai surfen masara tunda ba ubana dake kabari zan taso ya kai ba!" A hankali RAUDA ta sake tare hannunta tana kallonta a tausashe da yannayin tsarin halitarta ta ce" Ki ba almajiri ya kai zan biya, ki bi Ni bashi zan kawo maki" Dan tsura mata ido ta yi kafin ta juya ta fita tana sababi da aibata RAUDA, da yawan lokuta takan so ta kai hannunta jikin RAUDA sai dai tun ranar da RAUDA ta riki y'arta ta yi mata wani tsinanen duka dan ta ga Maman na zagin iyayen Rauda ana zama lafiya itama ta kalleta ta zageta ita kuma ta nuna mata bata da hankali Maman ta yi ta yi ta kwaceta ta gaza karshema da Raudar ta yi kukan kura ta hankade Maman da y'ar Tata sai da Maman ta fi wata tana zuwa ana murza mata bayanta dan ta baya ta je ta fada ta ji rauni sosai, shi yasa idan Raudar ta mike tana huci sai Maman ta ringa kiyaye abinda ke saurin sakata fita a hayacinta wato zagin iyayenta Mama na fita Abdul Hakim ya rukunkume Rauda yana fashewa da kuka ya ce" Aunty tsoronta nake ji, kasheni zata yi" Itama zuciyyarta ce ta karye ama ta ki nuna masa a hankali ta zaunar da shi ta zauna ta dora kansa saman cinyarta tana shafawa a tausashe ta ce" Dama Akoy wanda ya isa ya karar da kwanan wani in ba lokacin mutun ne ya yi ba? Haba boy din aunty, ka daina fadar haka ka ji? In sha Allah babu abinda zai sameka sai abinda Allah ya kadarta maka ka ji? Fada minda me zaka karya yau? Zaka je ka siyo ne ko na je na siyo maka? Yau zaka je makaranta kuwa an kanena?" Ajiyar zuciya ya ringa saukewa a jejere da sauri ya gyada mata kai ya ce" aunty zan je, kin ga Malamin mu na islamiyya yace ko me aka yiwa bawa ya barwa Allah, sakayar Allah ta fi ta kowa, Allah zai saka masa ya saka shi a aljanna ama kuma yace bawa ya kasance mai yafiya, na yafewa Mama aunty kin ji?" A hankali ta dauke hawayen gurbin idannuwanta ta lalubo kudin dake cikin rigar Mamanta ta mika masa dan idan bata saka kudi a nan ba tana kwonce za'a lalubeta a kwashe Abinda ta ajiye, gashi nauyinta da na Abdul Hakim a wuyanta yake, Mama na ikirarin hana masu abinci dama ba basu take yi ba ai a tausashe ta ce" Maza karbi je siyo mana abinda ranka ke so bari in zuba maka ruwan wanka idan ka dawo ka yi sai mu je na kaika makarantar daga nan na kaika wajen inna kaka zaka je?" Cike da farin ciki ya amsata kan zai je kafin ya mike ya tafi da gudu daga gidan danma kar ya hadu da Mama ko yayarsa su daki banza su kwace kudin A hankali RAUDA ta karasa bayi ta yi wanka da brush ta fito ta daura alwallah ta shige ciki dan gabatar da sallar da aka sakata yin lati dan dole, inda yar gidan Mama ta bita da kallo a lokacin da ta shige daure da zani daurin kirji cinyoyinta du a fili da cen wajen wuyanta da hannayenta dai da kuma gashin kanta Baki ta tabe kasa kasa ta ce" Du kyanki sai na auri mijin da ya fi ki in ji Mama, aikin banza kyan banza!" Bayan ta gama sallah carbinta ke hannunta tana ta istigfari, a hankali a hankali ta fashe da kuka tana hade bayanta da jikin bangon dakinsu mai dauke da dati, dan a gidan idan Akoy wajen ajiye kowani tarkace dakinsu ne, duk yadda ta kai da gyaran dakin a banza ne tunda datin cikinsa ya ishe shi A hankali take kukanta mai gunji da ratsa zuciya Shin ina zata saka ranta ne? Ina ake so ta kai kanta ne? Dan ta hadu da maraici shine ta yi laifi? Me ta yi da zafi? Tana bakin kokarinta dan gannin ta faranta ran Mama, ama ba zata taba cin arzikin mutuntawa ba bale arzikin a dauketa tamkar y'a? Me Mama take tunani ? Dama ita bata sakawa ranta zata yi aure ba a duniya saboda ba zata taba yin aure ta haihu ta mutu ta bar abinda ta haifa ya ga irin izinar da take gani na rayuwa ba, haka kuma bata taɓa sakawa ranta zata yi arziki ba, sai dai nacin da Mama ke mata na yau da kullum kan natawa cewar a duniya babu matsiyaci irinta dangin tsiya dan iyayenta da yan uwanta sun rasu a halin talauci wanda Allah ne ya halicce su haka Shikenan sai ya zama abin zagi? Idan ta samu zama irin wannan takan ji kamar zuciyyarta zata tsaya Ita a zuciyarta babu gurin farin ciki Babu gurin tunanin samun jin kai a duniya Mutun biyu ke sakata cenza tunani lokuta da dama BARA'ATU da ABDUL HAKIM, ita Bara'atu ta riga ta san lagonta har tana sakata daria da murna, shi kuwa Abdul Hakim yana da uwa da uba a duniya da dangi ama irin rayuwar da yake fuskanta mahaifinsa ya ki bada shi wa dangin mamansa ya sa ta dauka itace duniyarsa, itace uwarsa, ubansa danginsa Da sauri ta shiga share hawaye tana cire hijabinta ganninsa ya shigo da salama hannunsa dauke da bakar ledar da ya siyo kayan karin nasu sai farin ciki yake yi ya nemi waje ya zauna yana fadin" aunty harda kifin babale mai ayaba yau na siyo mana" A dole ta kakalo murmushi tana gyara zama ta ce"iyeah bari na wasa hakorana Sarkin cin dadi ya samo mana kayan dadi" Shima farin ciki ne ya mamaye zuciyarsa ya bude yana mika mata nata, da nasa sannan ya bata cenjinta Murmushi ta yi ta rike cenjin a hannunta tana tunanin yau ko da isheta zuwa wannan gagarumar restaurant din mai sunna ABUSA? dan tana so ta yi sabon kamu ko ta samu masu nauyi, ama kuma ba zata yarda ta tsaya daga nan ba sai ta samu baki ko uku ne yau din dan ta dan samu kudin ta ba Mama ko a bar mata Abdul ya kwana cikin nutsuwar zuciya ba zagi bare hantara Sunna gama cin abincin ta haɗa ledojin ta raka shi bakin bayi ta tsaya ya shiga wankan Yana fitowa ta bashi brush dinsa ya wanke bakinsa sannan ta raka shi daki ta kuma tsaya ya saka kayansa na islamiyya domin yannayin kwakwaluwarsa kin daukansa suka yi a boko , dan yannayin na Abdul Hakim sama sama ne Cikin nutsuwa suke Tahowa daga dakinsu zuwa falo tana rike da hannunsa yana magana kasa kasa Murmushi ta yi kasa kasa ta ce" Asalamu alaikum jama'a....mun zo maku da nagartacen ingantaccen maganin Ulcer, magani ne na Hausa jikake wanda Dubai suka gwada suka ji dadinsa, nagartatun tsatatatun itaciyoyin da suka bamu sasake masu anfani ne ake anfani da su, a nan jamhuriyar Nijar a garin Damagaran a farashi mai rahusa dubu biyu yan naija , yan nijer kuwa 1500francs mai bukata ga numbar +227 96897192 , HAJIA RAHAMA 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *AZAL!* 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *SAJIDA NIJAR* *PAID BOOK* _Bismillahir rahamanir-rahim._ *8* *wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nigar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍* *TALLAH, TALLAH, TALKAH* _*TOH TO TO!*_ 🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_ _Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_ Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake _Amarya_Uwar gida_ _Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_ _Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_ INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼 🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI* *🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU* _KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_ _SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_ 💁🏽‍♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻* 💁🏽‍♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI… _MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_ *ADRESSE 94536935 94.53.69.35* *Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER* KARKU BARI A BAKU LABARI🥳 Litattafan marubuciyar Duk karyar kada Yar mahaukaciya Bak'a ce Bani da zabi Daga tafia daukar soja Neman na kaina Kutkale Mage Bani da zabi Idan ka raina inda kake Umughuluk itifal Duk nisan jifa Wata kokowar Ni zan ladabi Dakika biyar Da ciwo a zuciyata Aure yakin mata Alkalamin Kadarata Dutse Daga tafiya daukar soja Makauniyace ND now *AZAL* Murmushi ta yiwa maganar da ya yi, kasa kasa ta ce" Ba Abul bane bawa, Abdul ne, kuma kai bawan Allah ne ba na mutun ba boyboy" Dan rabewa ya yi jikinta a lokacin da zasu fice sakamakon gannin Mama ta dosa falon Itama dakatawa ta yi har maman ta shige sannan suka fita kusan sunna sauke ajiyar zuciya a tare A Nutse suke tafiyar, tana rike da hannun Abdul har suka karaso kusan masalaci daidai inuwar su malam da su Liman Kamar yadda ta saba gaishe su a mutunce ta duka ta gaishe su sannan suka yi gaba Sun dan yi gaba kadan Muryar babansu ta saka su dakatawa suka juyo kusan a tare Da dan mamaki saman fuskarta ganninsa sanye da farar jalabiya kuma yannayinsa na nunin wanka ya yi harda kanshin turare ta ce" Baba?" Shima murmushi ya yi yana kawar da mamakinta, dan sarai ya karanci mamaki ne ya kamata ganninsa a Anguwa a irin wannan lokacin , a da idan suka yi fada da Mamansu ya koma gidan giya Kennan sai ya yi niya dan kansa ya huce zai dawo gidan Da kula yace" Ina zaku je?" Dan murmushi ta yi tana jin kamar kwallah na neman cika mata ido ta ce" Makaranta zan raka shi, daga nan na kai shi wajen inna ya masu kwana biyu in bai tada rigimar sai an kawo shi wajena ba" Murmushi baban ya yi cike da jin tausayinsu dan ya san saboda sun yi rikicin ne zata matsa shi nesa da ita kar Mamansu ta dake shi, yana laluba aljihunsa ya ce" Bari na ga ko na alewa na baka ɗan gidan auntynsa" A aljihunsa babu wani abun kirki ko kwondala babu dan bai yarda ya zauna da kudin da ya yi niyar yi mata siyayar kayan makarantarta a gudun kar matarsa ta sace kudin , Da yar kunya ya dubeta zai yi magana ta yi gagawar fadin" Baba munada cenji a nan fa, zan bashi ko Abdul din baba?" Abdul ya gyada kai yana bangalar darkyar da ta wuce misali yana kallon baban nasa, shi dai ya san babansa ne ama ba wata shakuwa a tsakaninsu sai ta shinfidar fuska, to yaushema baban ya zauna bale har ya wani shaku da shi? Umar sai ya ji wani iri a zuciyarsa, yarinyar nan ba aikin fari take yi ba ba baki ba, ama kuma a wajenta ake amsar kudi, ya Allah ka sa Rauda bata wasa da mutuncinta duk rintsi Kasa cewa komai ya yi sai jadada mata da ya yi yana wajen su liman , hakan ya saka mata farin ciki sosai a zuciyyarta suka tafi ita da kanninta a kafa har makaranta A lokacin da ya shiga ya zauna suka gaisa da malam yana ta faman yi mata annuri ta dawo karkashin shuka ta zauna dan sai an tayar da su ta kai shi wajen inna ta koma gida, ta zauna ta shiga contact dinta a hankali tana dubawa da son ganin wanda ya dace ta sakawa Hi, wanda yake nacin son ganninta kuma ta san idan ya zo baya tafiya bai yi mata ALKHAIRI ba A gaskiya ta irga mutane da yawan gaske, har sai da ta saki murmushi mai ciwo tana kallon cikin makarantar su Abdul a ranta ta ayana' Sai kace mai zaman kanta? Wannan ko mai sana'ar amsa a hannun maza ta biya masu bukatu ai sai haka, babu kalar wanda bani da shi Ni RAUDA ' , Sai kuma ta sauke ajiyar zuciya ta kore tunanin dan bata so ta dagawa kanta hankali a tunanin da ba zai fisheta ba Mutun biyu ta iya tabowa saboda ba zata tabo sama da haka ba ta haɗa su a kofar gidan su a yi abinda aka taba yi, ta haɗa samari aka shiga fada Mama ta rufe mata gida a ranar sai gidan makota ta kwana Mama tace ba zata saka a zo a kwasheta a kaita police station ba! Cikin ikon Allah biyun nan da ta zaba suka amsa gayatarta cikin dabara, domin babu wanda ta nuna da sanninta ta tabo shi, cikin yannayin kisar da ta koya dole dan ta kubutar da ranta ta iya yarda da son ganninta da suke yi da kyar, bayan ta shardanta masu tsakanin magariba zuwa isha'i da kuma bayan isha'i zuwa karfe takwas , dan daga nan ne zata je restaurant ta samu koda awa daya ne ta dawo gida , tunda Abdul baya nan bata da damuwar ta bar wani a gida bale ta dawo a gagauce, idan kuwa kwana zata yi a cen da wahala a gane bata kwana gida ba bale ya damu wani Sai da aka sake su daga makarantar ta raka shi gidan inna, a hanya suka sayi yan fruits suka jewa innar da shi Sosai inna take masa oyoyo tana dan goge masa yawun da yake dan zubarwa kadan ta rungume shi tana ta shiga RAUDA albarka tana fadin" Yau ya tuno Ni? Oh mijin Allah ya sa ka yarda koda kwana biyu ne ka min kar ka dora min rikicin aunty aunty" RAUDA na kallonsa ta ce" Zai zauna Inna in sha Allah, ko Abdul din baba?" Kai ya gyada ya shige dakan inna yana gigibo kayan wasansa da RAUDA ke kawowa ajiya nan in dai tana so ya mora, kaya masu yawan gaske dan da yawa ya wuce shekarun wasa da su ama ita idan ta gani sai ta kwaso ta kawo masa ta jibge, shi yasa a kulun inna dake matsayin kakarsa ta wajen uwa ke girmama Rauda da Binta da addu'a, ko mahaifiyarsa dake wata kasar tana aure a kulun idan ta samu halin yiwa Rauda alkhairi takan yi mata haka kuma tana Binta da addu'ar fatan alkhairi, dan ta mata komai da take kulawa da gudan jinninta Da dabara RAUDA ta tafi , gudun kar ya ganta ya ce sai ya bita Tana fitowa ta tari dan sahu ta masa kwatancen saloon din da take gyaran kai, wajen maman aisha Tana zuwa ta tarda mutun biyu ne gabanta dan haka ta zauna ta shiga chatting tana gannin kiran Atu ta ki dagawa dan ta yi alkawarin sai ta yi sati biyu cir zata je gidanta ta mata fatan ALKHAIRI sannan zuwan ya zama sai da dalili domin ba zata taba ajiye kafa gidan aminiyar Tata ba, dan gudun abinda ke iya je ya dawo Ana gamawa wace ke gabanta aka kama gashinta, A lokacin da ake caje gashin kanta sosai na sha mamaki, ashe dunkulewar nan da ta masa ta dunkule ainahin yawansa da kyansa da tsayinsa Wanke mata shi aka yi aka sakata cikin na'ura mai busarwa mai dumi sannan aka shiga gyara mata faratunnanta na hannayenta da na kafarta aka saka kafar cikin abin wankewa aka shiga wanke mata ita, dama bata da wani dati ama a haka aka wanke mata ita tassss har tana daukan santsi a takalmin da ta saka Hannayenta kuwa cikin wata na'ura mai dumi aka saka su suka dauki dan lokaci aka ciro mata aka sake gyara faratunnan sannan aka shiga warware gashin ana tambayarta abinda take so a mata da gashin Da dan murmushi ta ce" Maman A'isha kar ki masa komai daure min" Maman aisha ta yi yar dariya ta ce" Dama na sani, shin yaushe zaki fara kitso ne da gyaran gashi a yi masa kaloli? Ni da inada ko rabin gashinki ne da an shiga uku Murmushin dai ta yi ta bude bayan wayarta ta ciro kudinta ta bata ta mata Salama ta nufi gida a lokacin har yama ta yi sosai ana daf da kiraye kirayen magariba Bata tsaya bata lokaci ba wanka ta shige Tana fitowa ta daura alwallah ta shige dakinta ta kunna fitila da fanka ta rufe dakin Sallah ta gabatar ta saka wata doguwar riga ta zumbula hijab ta fesa turare sosai ta dan murza lips a bakinta ta dauki wayarta ta amsa kiran da kusan na biyar Kennan ana mata shi ta sanar masa cewar gatanan zuwa ta mike ta fita Bata wani jima a wajensa ba suka yi Salama ya zo mata da abinda suka yi magana ta waya dan ta sanar masa ne ba shi ta so kira ba sakonta take ta neman yadda za'a bata kafin ta kai kudin ɗinkin , cikin dabara dai ta yadda ba zai ce ta roke shi ba ta amso kudade ta dawo cikin gida tana ta tuna a lokacin da ya zo bata kudin sosai ya so shafar hannunta itace ta kiya saima da ta masa alkawarin zata neme shi yanzu bata so babanta ya dawo ya ganta a kofa ne ya yarda ya tafi da ta tabatar duk masifa sai ya yi wani abin ko shafata ko yace zai rungumeta koma sama da haka, dan abin yanzu ai kowa ya sani bani in baka ne soyayar in dai kwadayi ka saka a gaba Na biyunma sai da suka so samun matsala da shi, dan shi a kulun dama sai ya zo mata da maganar aure, shi aurenta yake son yi, da kyar ta salame shi ta dawo gida ta ajiye kudin nan ta shiga kimtsawa Cikin nutsuwa ta saka atampa riga da sket masu ruwan fari da ja da dan sirkin baki kadan, ta ciro takalminta mai dan tsayi kadan ta ajiye da jakarsa bakake sai dan yalolon mayafi baki mai shara shara sosai ta turare shi sannan ta sake kunce gashinta a hankali ta caje shi ta daure da dan ribom siriri baki sidik ta dauki jambakinta mai ruwan lebenta ta shafa ta ɗora masa man lebe kadan ta dauki wayarta baba ta saka a yar jakar nan da kudaden nan kaf ciki, ta sake yiwa kanta wankan turare sannan ta dauki wayarta karama ta yiwa mai adaidaitan dake kaita Anguwa da dare flashing ta fito a Nutse ta nufo falon tana jin Mama na yiwa y'arta fadan wai ko nata da saurayi ko mene? A hankali ta ce"Mama na tafi" Da sauri Maman ta kalleta, sai kuma ta dan tabe baki kadan ta ce" Sai kin dawo, kin dai san tarin bashin dake kanki, ki tabbatar da fitar ta maki anfani in ba haka ba WALAHI ina nan ina jiranki!" Dan murmushi ta yi ta fice ba tare da tace komai ba, Maman kuwa ta ja tsaki ta ce" yar gidan matsiyata sai dan banzan kyau uwa ita ke karra kera kanta kulun a daki, ki je ko nemo min dan kudin nan baki na zai zamo na banza ba ina ji ina gani!" Y'arta dake gefe ta tabe baki ta ce" Mama wai me yasa ita RAUDA kowama sonta yake yi ama Ni kina ta bani maganin farin jinni babu mai so na ko dai ba zan yi aure bane ni?" Bakin uwar ta bige mata tana fadin" Ke dilla tashi daga nan dan ubanki ki yi wanka, tun jiya nake bin kanki ki yi wanka ki wanke wandon nan na jikinki wari yake yi daga kin zo kan mutun ama kina min kunnen kashi, ke idanma an nemo na sai kin gyara ba zai kama ki? Ban san wannan tsinaniyar daudar a inda kika samota ba, gashi ki dan yi kama da Umaru baki yi ba kin kwaso kankanki baki bar komai na babanmu ba ke mace sai dati da tsami, ki yi wanka ki zo ki yi kwaliya ki dan zaga baya gidan su kawarki ki dawo ko a dace da wani rantsatsen ya dauke min na maki gadon yar gata" Tana tura baki ta cika buta daya da sabulu ta yi bayin kasa kasa tana fadin" WALAHI na zan yi wanka ba, shekaran jiya fa na yi, wani abinma ai barnar ruwa ne, wandona kuwa bashi da dati ko kadan abinda ba fitsarin kwonce nake yi ba bale ace na masa fitsari, wanke jikina zan na shafa turaren RAUDA da kayan kwaliyarta na ari kayanta na je na zo kafin ta dawo, ba dole a ki so na ba kin haifoni da muni!"........... 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *AZAL!* 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *SAJIDA NIJAR* *PAID BOOK* _Bismillahir rahamanir-rahim._ *9* *wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nigar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍* *TALLAH, TALLAH, TALKAH* _*TOH TO TO!*_ 🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_ _Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_ Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake _Amarya_Uwar gida_ _Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_ _Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_ INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼 🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI* *🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU* _KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_ _SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_ 💁🏽‍♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻* 💁🏽‍♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI… _MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_ *ADRESSE 94536935 94.53.69.35* *Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER* Litattafan marubuciyar Duk karyar kada Yar mahaukaciya Bak'a ce Bani da zabi Daga tafia daukar soja Neman na kaina Kutkale Mage Bani da zabi Idan ka raina inda kake Umughuluk itifal Duk nisan jifa Wata kokowar Ni zan ladabi Dakika biyar Da ciwo a zuciyata Aure yakin mata Alkalamin Kadarata Dutse Daga tafiya daukar soja Makauniyace ND now *AZAL* Daga nesa da watsetsiyar restaurant din ta saka ya ajiyeta sannan ta shaida masa duk rintsi kar ya yi nisa zata tabo shi A Nutse take jefa kafarta cikin takun salon tafiyarta mai tsarin gaske da ɗaukan hankali ta nufi hanyar shiga ta asalin Babar hanyar tana mamakin yau wajen babu tarin tarkacen yan mata da samari da cikar abubuwan hawa kala kala Mai tsaron kofar ne ya dakatar da ita yana fadin" Yau Akoy baki a ciki ba'a shiga ko tare kike da ita ISHAK?" A ranta ta ayyana ' Ku ga sakarci, ai yau ko wa ya siye wajen nan tunda na fito sai na shiga' A bayyane kuwa sai ta yi dan murmushi tana dubansa ido cikin ido ta ce" Tare muke mana, bai ce maka zan bane?" Gaba daya yannayin Rauda ya saka shi gaza yi mata gardama, irin sansanyan kanshin da take fitarwa da yannayin shigarta kuwa ya tabbatar masa tabas ita din kalar tafiyar manyan dake cikin wajen nan ce, dan haka ya kauce mata ba tare da ya ja ta wata maganar ba ya bata damar shiga ko tikitin shigar bata cira ba dan yau ai ba zancen ka ciri tikiti restaurant baki daya yau babu mai cin abincinsa sai wa'inda ke ciki sun tafi, dan yan oder kadai aka amshi odarsu, suma an fada masu sai fa daga bakin karfe goma sha daya zasu fara zuwa amsar abincinsu, duka kaf ma'aikatan wajen yau sun dukufa ne dan biyan buƙatar BIYA MARADI da bakonsa. Bata ji Dar ko daya ba a zuciyarta har sai da ta shiga filin da ake cin abincin idannuwanta suka sauka saman manyan kujerun dake ajiye da asalin VIP da mutanen dake zaune, gashi su dinma hanyar shigowar suke kallo, hankalinsu a nan wajen yake sunna fira ne kadan kadan , inda muryoyi biyu suka fi tashi ta ISHAK sai ta bakon Yusuf wanda ya masa ja gabar kawo masa wasu motoci tun daga Chaina a jirgi, motocin ne da yawan gaske kuma manyan motoci ba kannanu shi yasa abokinsa wanda suke harkar motar tare kampanin kerata ya ga dole shi zai kawo motocin ya biyo su a baban jirgin da ya sauka yau din a kasar ta Nijar, to tunda ya zo bai ci abinci ba, yace babu irin abincinsu shine Yusuf din ya kawo shi nan ya ci su wuce, domin daga nan cen park dinsa zasu wuce sai kuma ya sayi tiket komawa dan ba zama ya zo yi ba shima Bata san me yasa ba, bata taɓa tsintar tsigar jikinta da mikewa ko alamun jin tsoron shiga cikin duban mazama ba wai kwaya ukun cen da dake zaune ba sai yau, a hankali ta lumshe idannuwanta sakamakon jin Muryar wannan matar mai dauke da tufafin wajen tana fadin" Bismillah ki karaso" A hankali ta dan hadiye yawu gannin kusan su Dukansu dake kallon wani abin da wannan mai kama da kwai dan haske wanda du jan dan Chainar nan baya ɗaukan hankali kamar nasa yannayin fatar , yana sanye da wandon da za'a iya kira 3/4 damatsunnan kaffafuwansa a wani irin cike ga gashi kwonce jikinsu luflufluf , sai riga mai ruwan baki sidik karamar riga domin ta lafe a jikinsa ta bayyanar da yannayin jikinsa irin na mai abdo, harda wata sarka a wuyansa wace tashin farko ta ayanawa ranta cewa Christa ne suka dago jin an ce da mace ta karaso, ISHAK yana tunanin ko Nafisar ce ta shigo bayan ya fada mata idan aka bata damar shigowa ta tsaya daga baya ta yi kiransa ya taso bosss na tare da bako kar ta zo inda suke ta zo? Sai dai kafin ya idasa tunanin ya samu kansa da zubawa wace ke tsaye ido itama tana masu wani kallon da zuciyarsa ta shiga dokawa da gudu gudu Dawowar babar masu kula da bakin hannunta rike da wata kwalba da kuma wani kofi na kwalba fari kal mai dan tsayi ta ga Rauda a tsaye bata karasa ba ta samu kanta da tsayawar itama ta kalli Rauda ta juya ta kalli wajen su YUSUF ta karasa tana fadin" SIR ba bakuwarka bace wannan?" A hankali ya dauke dubansa tun kafetan da ya yi da ido ya kalli kwalbar jus din dake hannun matar zai yi magana Ishak ya rigaye shi yana fadin" Bakuwarsa kuma?, ba Bakuwarsa bace!" "Bakuwarsa ce" RAUDA ta fada a hankali a lokacin da ta karasa wajen kujerun da suke ta zauna a warariyar dayar dake facing dinsu tana hadiye yawun da ya kafe mata a baki dan ta samu kwarin gwuiwa " A karro na biyu ya sake zuba mata ido, ita kuma matar gannin bai bada umarnin komai ba sai kawai ta budewa Rauda kwalbar nan da abin budewa ta ajiye mata bata cire marfin ba da kofin a daf da ita saman wani dan table din ta juya dan kawo mata takardar abinda suke sarrafawa ta zaba Kirjinta ne ya yi wata irin bugawa sakamakon idannuwanta da suka shiga cikin nasa saboda tun dazun basarwa take ta yi danma kar ta yi ido hudu da wani ya koreta " *A salame su, bana son takura!, mu je mana bana son shirme zaka tsaya kana magana da yarinya ka salameta idan kana salamarta bana son takura* " magangannun da ya fada a shekaran jiya Kennan tun a wajen kaiwa maza abinci da wajen hanyarta ta dawowa gida A hankali ta ji lebenta na bushe mata Duda irin man leben da ta dan goga Kasa kasa ta yiwa idannuwanta tana jin wani yannayi mai kama da muzantuwa ko rashin jin dadin zama a haka a kusa da su da kokarin rasa kuzarinta har kunnayenta suka jiyo mata murya a shake ta Dan Chainar nan yana fadin" Wauh, a yau na yarda da maganarka ISHAK, da kake cewa kuma a nan Akoy yan mata masu classs da iya gyaran jiki, ban taba gannin buzurwa a nan da ta yi gyara irin wannan ba, ka ga wannan wani level ne da sai macen da ta san kanta take yi, mu a cen mun saka shi cikin Layin tarbiyyar Yayanmu, koyar da su zuwa ana gyara masu jiki a saloon, ka ga hannunta da kaffafuwanta ta yi manicure da pedicure, kalli fuskarta tamkar santsin kwai, lebenta ga alamun taushi ne da su, idanun........................." Kallon da YUSUF ke masa ya dan bashi mamaki har ya saka shi dan takaita maganarsa, dama ba wai wani zuuuuuuuuu bane yake yin maganar ba tsari, no a hankali ne yake yi sai dai duk abinda yake magana kansa ya kura masa ido ne kuma a hankali yake fadan cike da mamakin yannayin RAUDA da kuma yarda eh ashe da gaske ne a nanma Akoy yan mata masu classs haka Shiru ya yi a zuciyarsa yana tunanin ko dai budurwar YUSUF ce?, wannan duban ba dan kawai ya yi magana a kanta bane, ama da mamaki yaushe ya fara yin budurwa daya kwal? Ko a Chaina ai YUSUF mai yanmata ne bale a nan kasarsa Wani irin takaici ya rike mata zuciya a lokacin da aka bata dan litafin restaurant din dan ta zabi abinda zata ci, ba komai yasa ba sai gannin eh fa da gaske yau babu Sa'a a fitowar domin Wadinnan ukun ne kawai zasu zauna a nan din su isasu, sai kawai ta ba matar litafinta tana mata alamun ba zata ci komai ba ta maida dubanta kan ISHAK dake magana a hankali maimakun da dan karfi karfin da ya fara maganar dazu, yanzun kamar wanda baya so ta ji abinda ke bakinsa ya ce" Sir, na fitar da ita ne?" Bai san dalili ba, tambaya aka masa da Yaren da ya ji bayan Yaren mahaifiyarsa Larabci, ama sai amsar ta so gagararsa har ya dan zuba masa ido na yan SAKWANI ya ki ce masa eh ko aa, ya dai dauke dubansa ya maido duban nasa kan bakonsa ya ce" Wannan motar da ka gani ita nake so a kawo ama kwaya biyu, daya Moma zata hau, dayar kuwa Baban YUSUF" Yar dariya mutumen ya yi ya ce" Man kana ririta iyayenka fa, to ba za'a zuba su a park bane?" Kai ya dan girgiza kasa kasa sosai yana sake dago kaifafun idannuwansa ya ɗora saman hannunta a lokacin da ta amsa waya tana sauke kafarta da ta dora kafa daya kan daya ya ce" Sai sun hau kafin wani ya hau a nan" Kasa kasa RAUDA da zaman ya gundureta da tarin haushin mutanen wajen kansu take amsa wayar wani tsohon saurayinta wanda ta masa lakabi da 'ANDADI' , ba yaro bane, mutun ne mai shekaru sai dai kuma ba tsoho bane, a yadda ya fada mata shi Maraya ne gaba da baya, kuma wai bashi da Kani ko kanwa, mutumen maroko ne yanzu haka lambar ta kasar marokin ce ya yi kiranta da ita, ya yi ya yi ta gwada masa gidansu ta kiya har ya yi tafiyar nan a yadda ya fada mata zai je ne ya gama dukiyar iyayensa kaf ya siyar na SIYARWA na bayar da na bayarwa ya tattara ya dawo Nijar da zama ɗan yanzu maroko bata masa dadi tunda bashi da shakiki ko daya, ya jima a kasar Nijar yana dan jin Hausa da French sosai da larabci, ya nunawa RAUDA da gaske ya zo wajenta hakan ya sa ta sulube, dan ita kam bata ganta a duniyar aure ba , kuma fa zai kai uncle dinta a shekaru fa, ba zata so ta ja shi a kasa kamar yadda take jan kannanun samarinta, ama shi baya ji , ga kyauta irin mai gigitatan nan A Nutse ta mike tana jan dan mayafinta da ya sauka daga kanta ta mayar ta dauki jakarta ko ci kanku bata ce da su ba, hasalima ko sake kallonsu bata yi ba ta yi gaba cikin tafiyarta mai tsarin gaske tana amsa wayar a tausashe sunna magana da Yaren freinch dan da shi tana gane komai shima haka Dubansa ya dauke yana jin zufa na tarun masa a tafin hannuwansa, sai kuma ya bi bayan Ishak da kallo wanda ya mike har yana hade tafiyarsa ya bi bayanta "Man, rigima kuka yi da madame ne? Na ga ta zauna bata ce komai ba kuma ta tashi ta tafi?" Abokinsa ke tambayarsa bayan ya dan tabo shi dan gannin ya kurawa hanyar da suka bi ido Idannuwansa ya maido kansa, sai ya rasa gane yarensa, kwata kwata ya kasa gane abinda ya fada sai kawai ya budi bakinsa a Nutse ya ce" Ko a yi mana take away? I'm tired Man" Cike da gamsuwa cewar ya gajin ne dan gannin ya fara lulumshe ido ya nuna masa ai normal ne a hada masu abincin su tafi da shi Mikewa ya yi ya masa nunin yana zuwa ya nufi hanyar da Ishak ya bi haka kawai ba tare da ya san abinda zai tsinta a wajen ba da hannunsa ya yiwa masu dafa abincin magana ta biyo shi da sauri a hade ya furta" Ku yi emballer " Daga haka ya yi shiru ya ci gaba da tafiyarsa har kunnayensa suka ringa jiyo masa magangannun mace kamar wace ke kuka kamar wace ke cikin yannayin tashin hankali A hankali ya ja ya tsaya yana soke hannayensa cikin wandon dake jikinsa ya zuba masu ido su uku, ISHAK a tsakiyarsu, Nafisa na magana tana fadin" Walahi sai na kai kararki, me na maki? Me na yi maki? Ishak itace fa ta ji min ciwon nan shekaran jiya da ka kaini asibiti, dan kawai muna maganarta a mota ranar da muka kai maku abinci ta shakeni ta ja dan kunnena, kuma yanzu ta mareni? Ta fada na ciri tikiten fada da ita tunda na zagi iyayenta , hakan na nufin tana iya halakani walahi sai na kai kararta a mini tsakani da ita sannan na kaita fadar mai Damagaran ko ta sarki SANDA a mana tsakani da ita idan ita mahaukaciya ce Ni ba zan yarda ta kuma dukana ba, kema ki zagi iyayena mana dan kawai na zagi iyayenki?" Da karfi Nafisa ke maganar, hawaye na shatata a fuskarta dan a wajen da RAUDA ta dauketa da mari YANZUN a gefen wajen da ta ja mata shatine ne, har ga Allah ita bata ganta ba da bata bari ta cin mata ba, sai jin saukar mari ta yi a lokacin da suke rigima ita da mai tsaron kofar nan yace ba zata shiga ba wace ake jira ta jima da shiga, bata san mahaukaciya bace RAUDA da bata shiga harkarta ba, ama walahi sai ta kai kararta dan ba zata ci bulus ba, yaushe rabon duniya da fadan duka in ba wulakanci ba? A hankali Ishak ke fadin" Nafisa yi magana a hankali na fada maki bos na ciki fa , kin ga mu je waje na masu masalaha, ina amfanin fada yan mata da ku? Mu je waje na shirya ku na tabbata an samu rashin fahimtar junna ne......" Yana fada yana damko hannun Nafisa ne, haka kuma ya miko hannunsa da nufin riko na RAUDA, a hankali ta ja baya tana sakin lebenta na kasa da ta dantse tana dubansa ta ki yarda ya kamatan ta kuma ki yarda ta bi su Dakatawa ya yi yana kallonta, tsakani da Allah da farko niyarsa sai ya wulakanta yarinyar nan tunda ta ja masa tsaki a mota, ama a yau gaba daya tunaninsa ya sauya a kanta har ya zamto yana jin koda wani yace zai wulakanta ta ba zai barshi ba Da kula ya ce" RAUDA ko?" RAUDA ta sake kicin kicin da fuska ta ki bashi amsa A tausashe ya ce" Ki yi hakuri an bata maki, ki yi hakuri ta zage ki, mu je waje na sasanta ku, a nan bana so oga ya fito ya same mu cikin wannan halin ransa na iya bacewa, ki yi hakuri mu je waje ku sasanta kin ji?" Rauda ta dan tabe baki ta ki kama hannun da yake miko mata kasa kasa sosai ta bude bakinta cike da yannayin yangar da take ainahin asalin halitarta ta ce" 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *AZAL!* 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *SAJIDA NIJAR* *PAID BOOK* _Bismillahir rahamanir-rahim._ *10* *wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nigar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍* *TALLAH, TALLAH, TALKAH* _*TOH TO TO!*_ 🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_ _Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_ Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake _Amarya_Uwar gida_ _Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_ _Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_ INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼 🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI* *🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU* _KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_ _SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_ 💁🏽‍♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻* 💁🏽‍♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI… _MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_ *ADRESSE 94536935 94.53.69.35* *Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER* KARKU BARI A BAKU LABARI🥳 Litattafan marubuciyar Duk karyar kada Yar mahaukaciya Bak'a ce Bani da zabi Daga tafia daukar soja Neman na kaina Kutkale Mage Bani da zabi Idan ka raina inda kake Umughuluk itifal Duk nisan jifa Wata kokowar Ni zan ladabi Dakika biyar Da ciwo a zuciyata Aure yakin mata Alkalamin Kadarata Dutse Daga tafiya daukar soja Makauniyace ND now *AZAL* A Nutse ta ce" Ni babu inda zan bi ku, masalaha kuwa Ni da ita sai a gaban sarki wanda zai ja min kashedin kar na kuma in ba haka ba na rantse maki yanzu na fara tsaga fuskarki dan mai zagin iyayena ya zauna lafiya Dube shi duba, shima zan yi shiru ne ba zan amsa shi ba ama ba zan taba gannin girmansa ba...!" Da sauri ya sake zubawa fuskarta ido da yannayin furucinta ya saka shi kafe lebenta da ido har ta dasa Aya ta juya ta fice ta babar kofar hankali kwonce A hankali ya samu kansa da lumshe idannuwansa dan ya daidaita bugawar da zuciyarsa ke yi, yana bude idon ya ga Ishak ya rungume Nafisa a jikinsa yana bata hakuri da alkawarin tunda ta san gidan su RAUDA zasu je a sasanta su, ama ta kiyayi zagin iyayen mutun wasu fa a kan iyayensu mahaukata ne Kansa ya dauke sanadiyar wayarsa karafa fara da ta fara vibration Wayar mutun biyu kawai ke kiransa da ita, k Layinma su kadai suke da shi, mahaifiyarsa da mahaifinsa dan haka tana fara vibration ya zuba idannuwansa yana karanta sunna kamar haka *MAI MARTABA* Idannuwansa da suka dan cenza kala ya juyar a hankali ya daga kiran cen ciki ya yi Salama sannan ya saurara Salamarsa ya amsa da sauri ba tare da ya tsaya ja masa aji ba kamar yadda ya saba, hakan ya sa ya sake gyara tsayuwarsa yana sauraro "Uminka ce, tun jiya da dadare muka dan samu matsala ta shiga ta rufe, na zata zata bude min da safe , ta ki budewa na kasa hakura na sa aka kirawo mai gyara ya Bala min kofar shine na sameta ciwonta ya tashi, yanzu haka muna Clinik Nandu ta ki min magana shine nace bari in kireka na ga baka kirayeta ba yau" Tunda ya fara magana kirjinsa ke dokawa, zuciyarsa na neman balowa daga bakinsa ta fito waje Jin karshen furucin mahaifinsa bai iya ce masa komai ba sai katse kiran da ya yi har baya gani da kyau ya karaso inda su Ishak ke tsaye ya ce" Zan je Nandu Anmy bata da lafiya, ka kula da shi kawai, kuma kar ka zo ka san aba yana nan" Daga nan ya yi gaba da sauri bai ko tsaya ya kula motar da suka zo da ita ba dan ba zai iya tsayawa har su fitar da motar Ba su tsayar da shi, a inda yake ji yake yi inama yanada wata baiwa ta bacewa a bayana a inda ake so, da ya bace ya bayyana a jikin mahaifiyarsa Yana fitowa da sauri ya sha gaban wata adaidaita, bai tsaya jira ba ya zagayo ya shiga yana fadin" Clinik Nandu zaka kai Ni" Mai adaidaitar ya kasa motsawa saboda budurwar dake cikin adaidaitar zaune tana amsa waya Sannin kowa ne a garin Damagaran idan har mace na cikin adaidaita namiji ya tsayar da ita ba za'a dauke shi ba ko nawa zai ba mai adaidaitar sai in ita MACEN ce ta bada lamunin a dauke shi, dan haka cikin tausasawa mai adaidaitar ya ce" Ka yi hakuri malam ka tsayar da wata na dauko mace ce a ciki" A irin wannan lokacin gani yake yi yaushe zai fita ya tsayar da wata? Ta yayane? Gaba dayama ji yake yi tamkar bashi da jinni a jikinsa, dukkan wata gaba ta jikinsa ta daina aiki sai dokawar da zuciyarsa ke yi wace ta wuce misali wanda ya tabbata in har yanada hawan jinni to ya hau a yau Da sauri ya kalli macen da aka ce an dauko yana karkatawa dan lalubar kudin dake aljihunsa gaba daya ya ciro yan jaka goma goma sababi kal kal lokaci daya yana shaƙar kanshin dake jikin mayafinta haka kuma yana dubanta ya samu kansa da jin zai iya fada mata inda zai je ya san zata aminta su yi tafiya tare ko dan furucin da ya ji ta yi a kan *IYAYE* A tausashensa yana kallonta, sai ya ji nauyin niyar da ya yi na bata kudaden nan duka, bai san dalili ba, a hankali ya ce" Mahaifiyata ce ba lafiya, idan ba takura ki bari a ajiyeni" Bata taba jin damuwar wani bawan da bata sani ba na neman zama damuwarta sai yau Bata taba dagawa wani gardi kafa ba komai laushinsa da tsarin halitarsa ba sai yau, bata taɓa ragawa wani dan uzurinsa ta bar nata ba sai yau A hankali ta dauke dubanta daga saman fuskarsa ta ce" Mu je ka kai shi Aminu" RAUDA ta fada a hankali tana dauke dubanta a kansa Tuki Aminu yake yi a Nutse ba da garaje ba, A daidai wajen da zasu yi kwanar Nandu din kwanar da Nandun ke jikinta wani mai mota ya daki gaban adaidaitar ta su adaidaitar ta daku da jikin garu ama bata fadi ba, gabanta dai ya yi ratsa ratsa Mai motar so ya yi ya gudu, dan a lokacin da ya ga adaidaitar bata fadi ba da sauri ya so juyar da motarsa ya yi tafiyarsa dan wajen yana kusa da police station ne, baya son bata lokaci , yanzu za'a zo a shiga surutun sai an yi aune aune an ga waye marar gaskiya a yi ta BATAWA mutun lokaci Da karfi ya fito daga adaidaitar ya daga murya yana fadin " SANI ZAKWALAM!?" Wanda aka kiraya da Sannin sai da ya zarro ido jin Muryar da ta kirayeshi A rikice ya taka birki ya juyo da dubansa da kyau dan gaskatawa Ai kam tsaf ya hango biya muradi na masa alamun ya gansa sannan ya juya ya koma wajen adaidaitar Aminu dake kiran SUNNAN RAUDA, dan kusan su mazan direwa suka yi ama ita bata iya dira daga adaidaitar ba, ga dukkan alamu ta bugu dan gefen hannunta jinni yake yi sosai Da kyar ta ciro kafarta daya, tana shirin ciro dayar gaba daya jikinta ya kwashi rawa idannuwanta suka tafi luuuuuu suka rufe ta nemi dikuwa da kas Kusan a tare suka tare ta, mayafinta ya fado saman hannunsa hannayensa kuwa suka talabeta dan Aminu sakar masa ya yi domin kamar ya shi kusa da ita sosai Zuwa lokacin Duda dare ne wajen ya fara cika da mutane ana ta salalami, nan da nan aka fito da abin daukan marar lafiya dan a jikin garun asibitin ne aka maka su Karbarta suka yi suka yi gagawar dorata lokaci daya sunna danne wajen dake jinnin suka shiga turata cikin clinik din, shi kuwa ya daga kafa a hankali yana rike mayafinta a hannunsa idannuwansa suka sauka cikin na mahaifinsa da ya'yan mahaifinsa wato sarki da kanwarsa HAJIA A'isha, sai kuma Sani ZAKWALAM wanda ya kade sun shima ya fito daga motar yana faman fadin " oga walahi ban san kunne a adaidaitar ba, innalilahi Oga mu je ciki a duba ka dan Allah" A hankali ya so dauke dubansa daga kansu saboda a cikinsu babu mai binsa da tausashen kallo, sai dai ba dama a tsayen nan da suke idan har bai zo inda suke ba kamar ya wulakantasu ne baki dayansu Kallo daya ya yiwa Sani kasa kasa ya ce" Ka bari mana baka gannin Ubana ne?, ka je kawai ku karata da police" Daga haka ya karasa wajensu a Nutse ya furta" Barka da dare, yaya mai jikin?" Mai martaba ne kaɗai ya iya amsa shi, mahaifinsa gefen hannunsa dake dauke da jinni yake kallo a zuciyarsa yana tunanin ko shima ya ji ciwo ne?, HAJIA A'isha kuwa takaici tamkar zai kasheta, ba wata damuwa ko Dar, ba wani jin nauyi ko gudun a jita ta ce" Asibitinma da mace zaka zo YUSUF?, mahaifiyar taka a kwoncenma sai ka zo da mace dan ka nunawa duniya waye kai?" A hankali mahaifinsa ya kalleta yana jin kamar bai dace ba daga zuwansa ta hau shi da wannan balakin bayan ta ji ana fadin hatsari suka yi, shi wasu lokutan sai ya ga kamar tana nunawa son kai a lamarin BIYA MURADI, ta cika zakalkalewa da wulakantarwa da nuna tamkar laifinsa ya fi na y'arta da d'anta ne, nan fa suka zo suka raba rikicin auren y'arta, an yiwa yarinyar aure da yan watanni da wani kamilin dattijo ya kawo karar cewa yarinyar na hali na bin maza a cikin gidansa har a saman gadonsa, da aka titsiyeta ta nuna eh hakane kiri kiri dole aka raba auren take zaune daram cikin mutane, dayan kuwa kannin RISLAN ba'a cewa komai, lamarinsa sai addu'a kawai, katon barawo ne mai sata a kasa da kasa, sha ba'a magana, maganar bin mata kuwa a cikin masaraitarma sau nawa yana kawo MACEN da ba ta aurensa ba? Yanzu haka da jikarta daya tasa, ama sai ta ringa irin abubuwan nan haka , bai san me yasa take yin haka ba, a ƴaƴanta ita din da kanta RISLAN ne kawai mai sauki, shine mai dama dama mai kamanta rayuwa da jin tsoron Allah "Da sauki jikinta, ama tana son ganninka, tana daki na biyu ka je YUSUF" Mahaifinsa ya fada a hankali, da murya a rarrabe yana dubansa tamkar ba shi ba Yusuffff ya zuba masa ido na yan dakiku da karantar sabon salo, hakama yan uwansa baki daya sai suka zuba masa idon sunna mamakinsa Murmushi sarki ya yi a hankali ya dan dafa kafadarsa, ba dan komai ba sai dan dama shi yana fada masa ya fa kiyayi bakinsa a kan yaronsa ya ja abinsa a jiki shiriya ta Allah ce, shi dai baya ra'ayin mahaifiyarsa gaskiya, ta yiwu hakan ya samu nasaba da irin yadda mahaifiyarsu ta tsani mahaifiyar YUSUF din Ajiyar zuciya YUSUF ya sauke ya nufi cikin Asibitin, yana so ya ga yarinyar nan yaya nata jikin, ama ya fi jin sai ya ga mahaifiyarsa koda zai iya tunanin wani abin a irin wannan lokacin A sanyaye ya karasa gaban gadon Mama a lokacin da ya bude dakin ya zuba mata ido yana kallonta Murmushi ta sakar masa a hankali ta mika hannu tana masa alamun ya zo, lokaci daya kuma tana bin mayafin dake nade a hannunsa da kuma abin jinnin dake gefen rigarsa wajen damtsensa A hankali ta riko jinnin fuskarta na nuna alamun damuwa tana riko shi tana so sai ya hayo gadon nata tamkar wani yaro tana tataba jikinsa da hannayensa ta ce" Sajan, jinni ne a jikinka? Me ya same ka?" Sai yanzun ya ga ashe jinnin da dan yawa, sai ya ji dama ya wanke kafin ya shigo, dan a duniya idan kana so ka ga rikicewar mamansa ya yi koda atishawa ce, yanzu zata nemi fita hayacinta Da kyau ya zauna yana taba fuskarta dake danshin raba yana duba nata hannun mai dauke da abin karin ruwa ya ce" Rohi ba fa wani abu ya sameni na, hatsari ne muka yi a adaidaita, yarinyar dake cikin adaidaitar ce ta bugu, ama ba sosai bane ba fa" "Yarinya?, ya Salam, budurwarka ce? Ya Allah, ina take ne? Sajan tana ina ne?, ya Allah ga jinni a jikinka ance yar buguwa, Allah ya sa ba wani abu ya samu y'ar mutane ba, tana ina ne? Kaini in ganta" mamansa ke fada tana alamun son sauka daga gadon ita da karrin ruwa ke jikinta hankalinta tashe Zuba mata ido ya yi yana jin nutsuwa da tarin kauna marar misaltawa a zuciyarsa, a hankali ya rikota da hannayensa yana son sai ta nutsu ya ce" Mahmah, ba fa abinda ya sameta, buguwa ce a hannu tana wajen likitocin, ba budurwata bace, adaidaita ne kawai muka hada da ita ina gagawar zuwa na Ganki, Please kar ki cire karin ruwan ke da ba ce lafiya gareki ba?" Sai a lokacin ta kalli karrin ruwan, kai ita fa tunda ya shigo ta ji ta warke daga dukkan wani abu da ya tsaye mata a kirjinta , ko yanzu zuwan su sarki da A'isha Sarkin kawai ta iya amsawa gaisuwar da ya mata, yau shine harda tambayarta jiki? Kwarai ta yi mamaki , A'isha kuwa ta zo din ama bata jin lokacin da ta tambayeta jikinta ba, itama bata bukata, dan ta riga kuma ta rantsewa kanta ba zata kuma daukan wannan wulakancin na A'isha ba! Sai da ya tabbatar da jikinta da sauki sannan ya barta bayan ya sheda mata lekawa zai yi ya ga jikin yarinyar, ita dinma ji ta yi dama zai yarda ta cire karin ruwan su tafi, sai dai ta san yanzu kuma ya zo ba zai yarda da komai ba , sai ta bi tsarin likitoci koda bata so dan ya zauna ya nemi tayar mata da hankali ba komai bane a wajensa a kan lafiyarta Aminu ya samu tsaye a kofar catégorie din da aka saka RAUDA Da sauri ya dan duka yana ba YUSUF din hannu dan a dazu bai san waye ya dauko ba sai yanzu da aka gama komai na lafiyar Rauda aka sheda masa wanda ya dauko din, hakan ya bashi mamaki ainun Da kula sosai YUSUF ya ce" Tashi mana, yaya jikin ta? Ka santa ne?" Aminu ya dan dago din ama ya kasa mike kafadarsa da ta Yusuf din dan girmamawa ya ce" Alhamdulilah da sauki sun sakata barci dai, na santa biya muradi yar anguwarmu ce, Ni kuwa Ni ke mata dan sahu kulun" Yusuf ya bude dakin ya shiga yana sauke idannuwansa a saman kanta, tana kwonce lambak tana barcin da karin ruwan ke sakata, an daure wajen da ta ji raunin an dan sasabto mata rigarta sosai Dauke dubansa ya yi ya kalli Aminu ya ce" Ka je ka sanar a gidansu, tunda da wahala su barta ta koma gida yau" Aminu ya yi tsai ya rasa abinda zai fada, a zuciyarsa kuwa tunani yake yi waye zai fadawa? Babu wanda bai san Rauda da rayuwar da take yi a gidansu ba, ba zai so Maman Rauda din ta zo nan ta wulakanta ba a cikin mutane, dan haka ya ce" Gidan nasu ne ba kowa ai Sir" Ido ya sake zuba masa yana son gane yarensa, wani irin gidansu ba mutane? Kasa hakura ya yi ya ce" Ban gane gidansu ba mutane ba, ina mahaifiyarta ne? In ba mahaifiyarta ai Akoy mahaifinta......ko yan uwanta????!" Fuskar Aminu nan take ta nuna alamu na raunin maganar dake bakinsa, a rayuwa yana tausayawa Rauda kuma yana yi mata fatan alkhairi, shi da ace yana da dama walahi da ya raba Rauda da rayuwar gidansu, Rauda kusan kowa a Anguwar nan na tausaya mata dan yarinya ce mai mutunta kowa, idan zata wuce sai ta gaishe da kai ko me kake yi, fuskarta da sakewa , du irin ukubar da take gani tana matukar jurewa bata bari tana yawan nunawa kowa ba, in dai ka santa ka san me take gani a gidansu ita da kanninta, Rauda tana gannin jarabawar rayuwa kala kala , a da laifinta ake gani saboda mama ta bi kowa ta fada masa bata ji sai yawo sai menene, sai dai yau da gobe ta wuce wasa kowa sai da ya ga asalin wacece Mama aka dawo daga rakiyarta ake kallonta da halinta A raunane sosai Aminu ya ce" *bata da iyaye biya muradi, sun rasu a hanyarsu ta dawowa daga kauye da yan uwanta*" Dukansa ne maganar ta yi? Ko menene ? Bai san lokacin da ya kurawa Aminu ido na yana kallonsa da bugawar da zuciyarsa ta yi "A yanzu haka tana rayuwa gidan kannin mahaifinta ne, shi kuwa ba mazauni bane, matarsa din kuwa idan har ta zo nan zata daga hankalin marainiyar Allah ne, idan har ba damuwa Ni sai in kwana a waje da safe zan rakata in fada, Duda ba lallai ta yarda ba ita maman nata" Aminu ya idasa fada yana sada dubansa daga na cikin idannuwan Yusuf A hankali Yusuf ya juyo da dubansa kanta ya zuba mata ido.... Gashin kanta a barbaje yake saman matashin kan da aka dora kanta, Fuskarta a sake take sosai , lipstick dinta har yanzu yana nan saman jan bakin da ta dan shafa Idannuwansa ya janye da nufin juyawa suka sauka a kan kaffafuwanta dake bude, farare tas tas da su har faratunnanta tas tas da su , harta tafin kaffafuwanta a idannuwa kawai idan ka kalla zaka ga mai tsafta ce ita din ko halitarta ce haka, dan luwai luwai suke abin shiga ido Dauke dubansa ya yi ya sake duban Aminu da furucin dake saman lebensa ya ji kamar maganar na neman yi masa nauyi Tambaya ce a bakinsa Tambaya ce a harshensa So yake yi ya yi tambayar So yake yi ya karra jin bayanin abinda bai shafe shi ba So yake yi ya ji me Kennan? Yannayinta na iya tashi tsaye ajiye shi a wata matsaya guda , itace irin ya'yan nan ne sangartatu da iyaye suka lalata take gannin daidai take da uban kowa A dazu furucinta a kan iyayenta ya saka shi tunanin eh lalle iyayenta bata haɗa su da kowa sunna gida ba zata yarda dan ta fito yawace yawacenta a zage su ba! A yanzu kuma sai, sai, sai yake jin kamar numfashinsa zai tsaya a kan son Sannin *WACECE ITA, ME YASA TAKE IRIN RAYUWAR NAN?* , sai dai ya gaza tambayar Aminu, kwata kwata bin digigin nan ba halinsa bane, abin nan bai shafe shi ba A tausashe bayan ya lumshe idannuwansa ya bude a kan Aminu ya ce" Happy juma'at mAh people 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *AZAL!* 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *SAJIDA NIJAR* *PAID BOOK* _Bismillahir rahamanir-rahim._ *11* *wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nigar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍* *TALLAH, TALLAH, TALKAH* _*TOH TO TO!*_ 🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_ _Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_ Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake _Amarya_Uwar gida_ _Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_ _Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_ INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼 🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI* *🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU* _KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_ _SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_ 💁🏽‍♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻* 💁🏽‍♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI… _MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_ *ADRESSE 94536935 94.53.69.35* *Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER* KARKU BARI A BAKU LABARI🥳 Litattafan marubuciyar Duk karyar kada Yar mahaukaciya Bak'a ce Bani da zabi Daga tafia daukar soja Neman na kaina Kutkale Mage Bani da zabi Idan ka raina inda kake Umughuluk itifal Duk nisan jifa Wata kokowar Ni zan ladabi Dakika biyar Da ciwo a zuciyata Aure yakin mata Alkalamin Kadarata Dutse Daga tafiya daukar soja Makauniyace ND now *AZAL* A tausashe , bayan ya lumshe idannuwansa ya bude a kan Aminu ya ce" Ka je wajen ka kwana, ina fata kai baka ji rauni ba?" Aminu ya amsa masa cewar shi bai ji ciwo ba sannan ya fita ya samu wasu maza dake jinyar babansu ya zauna wajensu yana ji a ransa ba zai iya tafiya ya barta ita kadai a asibitin ba, ko mahaifiyarsa ya fadawa ga inda ya kwana ya tabbata zata tausaya mata, kowama yana son taimaka mata, marikiyarta ce tamkar kwalba wajen Shari, tana iya hada maka wani balakin dan kawai ka taimaki Rauda din YUSUF kuwa bai bar dakin ba sai da ya daidaita abin kusan gadon dake iya shaidawar tashinta, haka kawai ya dan sake zuba mata ido kafin ya fice ya je wajen doctern da ta dubata suka dan tattauna ta sake tabbatar masa a asibitin ana kwana ana leka mararsa lafiya ne, idan ta motsa lalle za'a san motsinta koda abin karaurawar bai yi kuka ba Daga nan ya koma wajen mahaifiyarsa ya zauna saman kujera sunna taba fira har mahaifinsa ya shigo shima ya zauna saman wata kujerar , nan YUSUF ya mike da nufin tafiya sai mahaifin nasa ya umarce shi kan ya zauna , bayan ya zauna din ya zamto mahaifin nasa na dan hiratarsa, hakan ya sa mahaifiyarsa sakewa sosai tana ta yiwa mijin nata fira, dama ance mai d'a wawa , mahaifin YUSUF sai a lokacin ya samu salama da kwonciyar hankali a zuciyarsa yana tuna yadda suka rabu da A'isha, domin a wajen so ta yi ta ci gaba da zazagin Yusuf gaba daya sai ya ki saka baki, karshema sai ya ce ai sai hakuri da addu'a Allah ya shirya mana shi ya fi ALKHAIRI da la'antar, tunda ya fadi hakan sai ta ringa binsa da wani irin kallo , ko na menene? Allah masani, wani lokacin yakan so yarda da wata magana da abokinsa ya taba fada masa, Akoy wani lokaci da suke jaje irin na familly da rashin jin ya'ya dai da sauransu da abokinsa kuma uban gidansa Mai Damagaran, a ranar ne ya ce da shi" HONORABLE, a cikin yayanka ka kiyayi gagawar furtawa YUSUF wasu kalaman, ka kuma yi kokari ka ringa taro rashin jinsa, domin ku so ko ku ki YUSUF sai ya gaje ku!" A lokacin ne yace da shi" Mai martaba YUSUF dai nawa? Ai Yusuf ba zai taba duban sarauta ba, ka ganshi a nan ya fada ya kuma fada cewar mu rike kayarmu, ta yaya muke tunanin shi zai zo ya ringa zama gwamnati na masa albashi? , yace idan bamu sani ba mu sani shi ya wuce jiran dauka da umarni daga gwamnati, cewa fa ya yi tunda ya zama karamin kwari gwamna na iya yin yadda ya so da sarki ya rainawa sarauta wayo, ka san shi matsalarsa duk abinda zai ja masa wani raini ko halin karanta baya ciki, gashi Allah ya taukaka shi a cikin kankanin lokaci, a yanzu idan ka ji wanene YUSUF sai ka yi mamaki, ko mu mun san Allah ya dasa shi, sarauta kam idan da rabon Yayanmu sa hau da wuri ta yiwu sai dai RISLAN" Shine mai martabar ya yi murmushi yace da shi" ba'a cenzawa tuwo sunna komai gyaran da zai sha, gaskiya kuma zanen dutse ce, kai ka san jinnin da ya isa ya hau , tunda kuka yarda muka san da lauje cikin nadi a je a dawo koda kasa ta bini idonmu Akoy kundin labari, arzikinsa kuwa dama haka ake so sai ya ciyar da talakawa da shi, ama fa ya dace kanwarka ta farka daga barci domin *ZAKARAN DA ALLAH YA NUFA DA CARA* ko ana ruwan muzuru sai ya yi" A hankali Hon BELLO ya dan juyo ya zubawa YUSUF ido A zaunen da yake mayafin Rauda ne a hannunsa yana dan gogawa a wajen hancinsa wanda shi da kansa bai san asalin turaren dake jiki yake shaka ba, shi dai ya rike yama manta na MEYE abin dai a hannunsa kamar nasa haka ya masa rikon gaske Suturar dake jikinsa yake kallo har zuwa sarkar dake wuyansa yar siririya mai ruwan ash, ko karfe ce ko azurfa ce? Wa ya sani Damatsunansa da suka shake a cikin rigar nan ya zubawa ido har zuwa ƙafarsa dake cikin takalmi kafa ciki ama ba mai nauyi ba Agogon hannunsa ya zubawa ido da dayan hannunsa dake cikin na mahaifiyarsa a hankali yana kallonta tana ta labari yana murmushi Murmushin ya samu kansa da saki yana dauke dubansa daga kansa Abu daya ya sani shine da wahala YUSUF ya wulakanta a duniya, da wahala ya wulakanta saboda baya haɗa su da kowa, bai taba yarda ya haɗa soyayarsu da ta kowa, rabonsa da siyan shinkafar gidansa har ya manta, idan ya bada kudin cefane niya ya yi dan badangarci, ya jima da dauke masa hidimar kannensa, ya jima da fito da mahaifinsa cikin manyan kwarin kasa, domin a kasar Nijar baki daya a yanzu mutanen dake mu'amala da shi, shi da kansa ya san dan tsaya masan da yaronsa ya yi ne ba dan shi karfinsa ya kai cen ba, domin a yadda duniya ta zama idan kai ba kowa bane baka da fada a ji a gaban kowa hakan ne, shi BELLO yana da damar shiga inda ya ga dama a lokacin da ya ga dama idanma bashi da sanaya da mutumen da zarar ya fadawa YUSUF za'a neme shi ne yana zaune a saman gadonsa, lokuta da yawa shine ke yiwa sarki hanyar halartar wani taron , a yanzu dai a Nijar duk wani baba yana daukan mota ne a park din YUSUF, hakama a wasu kasashen makota, YUSUF ya mallaki park park da dama a garuruwa, kuma duk wata babbar mota yana yi mata nata daban ne, ya jima da shiga cikin duniyar bada kwongila a tsarin gwamnati, mutun ne mai nema ido rufe kuma a kulun habaka kasuwancinsa yake yi , ya ki ya matsa daga Damagaran da garin mahaifinsa ne saboda iyayensa, A hankali mahaifinsa ya ringa jin wani abu mai kama da kunya da jin nauyi Shin dan sun haife shi ne suke wulakanta shi haka? Kwarai matarsa tana da gaskiya ya dace ya fara yiwa kansa wa'azi ya duba abinda yake ciki da yaronsa Daren dai, shi bai samu rintsawa ba, domin YUSUF mahaifiyarsa na yin barci ya KWONTAR da kansa a saman gadon hannunsa cikin nata, dayan kuwa rike da mayafin Nan barci ya dauke shi, shi kuwa ya yi gadinsu har aka fara kiraye kirayen sallar asubahi Farkawa YUSUF ya yi yana yin hama kadan hadi da son bude rinanun idannuwansa ya sauke dubansa cikin idannuwan mahaifiyarsa da kuma mahaifinsa dake daf da ita yana taba goshinta da wuyanta Murmushi ta sakar masa, haka shima ya mike ya nufi bayi yana dan sake mikar da jikinsa dan jin du ya ririke Kulawa ya yi da kansa ya dauro alwallah ya fito yana jin jikinsa du a ririke saboda rashin wanka da brush Yana soke mayafin Nan a aljihunsa mahaifinsa ya karaso ya mika hannayensa yana cire masa sarkar nan dake wuyansa Yana cireta ya saka a aljihunsa kasa kasa ya ce" Mu je masalaci" Kallon fuskarsa yake yi da mamaki harda tunanin toh fa, sabon salo MEYE wannan din kuma? Ko dai shi din ma bashi da lafiyar? Shi kuwa ya yi gaba yana boye yannayin da yaron nasa ya shiga a ransa suka ba Nurse din damar shiga ta taimakawa Mama ta yi wanka da alwallah da sallah , wace ta nuna yanzu kam zata iya jikinta ya warke ba sai an kamata ba, ama Duda haka likitar ta ki tafiya tana kula da ita har ta gama aka gama gyara dakin nata aka saka turare mai sanyin kanshi aka barta A waje kuwa sunna gama sallar ya fito ya je wajen da Ishak ke tsaye da manyan ledoji dauke da kayan abinci da su fruits Nuna masa ya yi ya bashi dan mahaifinsa na nan kuma baya so su dagawa mahaifiyarsa hankali a kan wannan Jiki ba karfi Ishak ya bashi ledojin ya koma cikin motar da fatan samun lafiya wa mahaifiyar YUSUF din tare da fadin yanzu direbansa zai kawo masa motarsa da tufafinsa a ciki sannan ya tafi da ky din gidan a hannunsa Yana juyowa ya ga Hon BELLO tsaye kofar asibitin yana kallonsa, zuwa lokacin haske ya fara yi sosai a garin Fuska ya hade dan ya riga ya san yanzu zasu hau sama su fado, domin ya ga Ishak din da yake gudun ya gani Yana isowa kunnayensa suka jiyo masa Muryar mahaifinsa yana fadin" Me yasa ya juya?" Dakatawa ya yi yana kallon mahaifin nasa, ya sake kallonsa da kyau sai kuma ya dan dauke dubansa ya ce" Yana da uzuri ne" Murmushi Hon ya yi ya mika hannayensa ya ce" Kawo na rage maka kayan" Wannan karon kasa boyewa mamakinsa ya yi, har ya dan ja baya kadan yana kallonsa kafin ya ce" Me yake faruwa ne?" Hon Bello ya zuba masa ido ya ce" A ina fa?" YUSUF ya sauke ajiyar zuciya ya ce" Na ga yanzu Bama gabanta , kuma ka ci gaba da wani abin daban Abu" Murmushi ya yi yana riko ledar dake dauke da jus ya ce" Bani Ni haba ya ina so in taya ka kana wani kiyawa" Baki ya saki yana kallonsa, sai kuma a hankali ya ce" Ina son dibarwa wannan yarinyar da ta kwana a nan" Yana fada ne yana nuna daidai dakin da RAUDA take, daidai lokacin ne kuma Raudar ke cikin fadan a cire mata abinda yake hannunta gida zata je, Aminu sai faman kwatanta mata yake yi ama ta nuna masa ta ji sauki gida take so Samun kansa ya yi da nufar dakin ya murda ya shiga kai tsaye yana sauke dubansa a kan Aminu dake tsaye, da Nurse din dake tsayen itama rike da dan kwanon nan nasu na likitoci, sai RAUDA dake tsaye rike da abin gado sai luuuuuu take yiwa ido saboda abin magani ama fadi take yi gida zata je a salameta "Me yake faruwa?" Ya iya furtawa bayan ya kare mata kallo ya juya yana kallon Nurse din da Aminu Nurse din ta ce" Sir, zuwa na yi dan na cenza mata karin ruwan nan, na tarda ita ta farka shine tace ba za'a saka mata ba gida zata je yanzu yanzu" YUSUF ya kalleta da dan mamaki a fuskarsa ya ce" Ke da baki da lafiya zaki tafi gida?" Idannuwanta ta dauke daga fuskarsa tana saukewa kan Aminu, a raunane ta ce" Ina son gida Aminu, ta yiwa uncle a gida ya kwana yana nemana, Ni gida zan je!" "Ki yi hakuri y'ata a cire maki sai a kaiki gidan, zauna a cire maki" Abu ya fada a tausashe yana karewa Rauda kallo da son karantar yannayinta Ajiyar zuciya Rauda ta ringa saukewa ta zauna saman gadon, hakan ya sa sket dinta tatarewa sosai har kamar cinyarta dake fara sol zata bayyanar da kanta, duk kuwa yadda ta yi dan ta rufe jikinta hakan ya gagara sai kanta da ta sada kasa cike da jin kunya da takaicin zaratan mazan dake dakin a irin wannan lokacin jikinta na son bayana Har dan dukawa Nurse din ta yi wajen amsa umarnin Hon ta karasa ta cirewa Rauda sannan ta saka abin goge jinnin nan ta goge mata ta danne mata da auduga Da kula sosai Abu ya dubi Aminu, zuwa lokacin Yusuf ya fice ya nufi dakin mahaifiyarsa , ya ce" A me kuka zo ne?" Aminu ya ce" Sir, ai da daidaitar tawa ce aka yi accident din, tana nan police station sun ce idan an gama fitar da sakamakon wanda bashi da gaskiya nima sai sun buga min takarda na biya diyyar yawo da ita ba awo, zamu tsayar da adaidaita ne" Hon ya dan gyada kansa ya laluba aljihunsa ya ciro abin saka kudinsa ya ciro kudi masu dan kauri ya bashi da kula ya ce" Ku shiga ku je, sannan ka sanar min gidan su yarinyar zan zo da dare dan na basu hakuri na sanar masu hatsari ne kuka yi , Ni da YUSUF in sha Allah" Sosai Aminu yake godiya, yana so ya nuna masa ba sai sun zo ba dan kar su ga wulakanci gurin Mama, sai dai ya kasa fadin hakan, Rauda kuwa a lokacin ta shiga wanke bakinta koda da bakin ruwa ne, dan ji take du a takure, Bama kamar jikinta ji take yi kamar kazantar duniya ta tare a kanta Yana ficewa ta fito tana tambayar Aminu wayarta da mayafinta da pos dinta Ya bata wayar da pos din, ama bai san inda mayafin yake ba, dan haka suka fice tana jinta wani iri duda a garin yan mata na fita ba mayafi, ba wani abin bane a garin A cikin asibiti kuwa Abu na karasawa dakin ya samu YUSUF zaune yana ciyar da mahaifiyarsa wace take zaune itama ram da ita tana masa fira yana murmushi Yana shigowa YUSUF din ya zuba masa ido, idannuwansa cike da yannayin son yin tambaya, ama ya gaza yin, shi kuwa Hon karantarsa ya yi tsaf sannan ya nemi waje ya zauna ya bude wani abincin da kula ya yi bismillah kafin ya kai bakinsa ya ce" To wai haka ake yiwa budurwa? Sai ka tafiyarka dan tana rigimar gidansu za'a kaita? Lalabasu fa ake yi ko su dagawa mutun hankali walahi" Dan dakatawa ya yi da son kaiwa mamansa abincin a bakinta ya dan kallo mahaifinsa, kasa kasa ya ce" Ba budurwata bace" "To ama kama sonta ko?" Ya katse shi da son lalle sai ya ja shi surutu Da sauri ya dube shi, sai ya samu kansa da sakin dan murmushi dan sarai ya kula wani sabon salo ke dawainiya da mahaifinsa wanda ba zai sakankance ba sam, a hankali ya ce" Allah ya raba Ni da soyaya, adaidaita fa muka hada, ana ta wani bata hakuri tana shirme ai sai a barta ta yi yadda take so!" Ido Abu ya dan zarro, ya ce" Kai, ikon Allah, aya, Ni kuwa ta bani tausayi, kuma kamar tana tsoron kar iyayenta su ga bata dawo gida ba, sun tafi dai yanzun da dare sai mu je mu na iyayen nata hakuri mu fada masu a inda ta kwana dan ga dukkan alamu bata saba kwana a waje ba gaskiya" Mama ce ta ce" Yarinyar da suka samu hatsari ko Aban YUSUF?" Aban Yusuf ya amsata, ta ce" Nima fa na so gannin jikinta dan nan ya shigo da jinninta a jiki, dole ta damu iyayenka ba cen sunna cigiyarka, Ni da nice ai ba zan iya barci ba sai na ga yara mace ta dawo gefena ta kwonta, karma su daketa su ƙi yarda Ni walahi dama rakata ka yi ranka shi dade" A hankali Yusuf ya sake debo abincin ya nufi bakin mahaifiyarsa da shi a ransa yana ayana' anya kuwa damuwarta gidan ne? Koda yake ance tana da Kani ko?, a da ba zan bi Abu gidansu ba, but zan so na ga marikiyartar nan da idona!' Haka suka ci gaba da fira hankali kwonce har likitan Mama ya zo ya salameta suka nufi gidanta Tafe suke cikin adaidaitar ita da Aminu , dan ba yadda bata yi da shi kan ya je zata zo ya kiya ba, domin bata so ganninsu tare ya jaza masa wata fitinar ama sai ya nuna mata ko daya zai rakata su je tare sai su fadi abinda ya sameta ko dan marikinta kar hankalinsa ya tashi Banki suka je, ta sauka ta shiga dama idan zata fita duk wani abinta mai mahimmanci da ya shafi katin shedar yar kasa ne, katinta na banki ne takan fita da su saboda tsaro , takardun ta na makaranta kuwa dama a gidan inna suke da na haihuwa da sauransu domin akoy ranar da ta taba barin takardun ta na makaranta aka saka masu wuta akace ba'a san an bar fitila mai kananzir a wajen ba........ 😍😍😍😍☹️☹️ 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *AZAL!* 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *SAJIDA NIJAR* *PAID BOOK* _Bismillahir rahamanir-rahim._ *12* *wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nigar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍* *TALLAH, TALLAH, TALKAH* _*TOH TO TO!*_ 🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_ _Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_ Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake _Amarya_Uwar gida_ _Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_ _Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_ INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼 🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI* *🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU* _KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_ _SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_ 💁🏽‍♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻* 💁🏽‍♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI… _MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_ *ADRESSE 94536935 94.53.69.35* *Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER* KARKU BARI A BAKU LABARI🥳 Litattafan marubuciyar Duk karyar kada Yar mahaukaciya Bak'a ce Bani da zabi Daga tafia daukar soja Neman na kaina Kutkale Mage Bani da zabi Idan ka raina inda kake Umughuluk itifal Duk nisan jifa Wata kokowar Ni zan ladabi Dakika biyar Da ciwo a zuciyata Aure yakin mata Alkalamin Kadarata Dutse Daga tafiya daukar soja Makauniyace ND now *AZAL* Tana shiga ta je layin cirar takarda ta cira ta saka hannu a abinda take da bukata ta kai ta ajiye ta shiga layi, basu da yawa kasancewar safiya ce kuma Laraba ce ba mutane sosai , su hudu ne a layin daukan sako A hankali layinta ya zo ta shige dan dakin ta gabatar da dukkan abinda ake so sannan ta zauna aka duba mata kudaden A lokacin da aka sanar mata ko nawa ne a cefa sai da ta dan zarro ido dan mamakin yawansu sannan ta saka aka bata ƙadan a cikinsu , jaka dari biyar ta samu wata leda ta daure cif ta fito ta shiga adaidaitar tana tunanin lalle zata siyawa Aminu wata adaidaitar idan ta siyawa Uncle dinta abin hawan shima in har ta fada masa daga inda kudin suka fito in zai amince, domin ta san waye uncle dinta a kan lamarinta da samari, sam baya so tana amsar kudin kowa, yana yawan ce mata ne Rauda duniya ta lalace, ki daina amsar silen kowa, dan ba kowa ke kyauta dan soyaya ba a wannan zamanin na yanzu, da yawa zasu baki ne dan suma su nemi lalata ki, duk rintsi Rauda ki kama mutuncin kanki dan gobe na yi alfahari da ke kin ji?, ire irin abinda yake fada mata kennan idan yana cikin halin da ba na maye ba in ya ga kudi a wajenta, dan ya san bata siyar da komai, duk inda kudinta zai fito daga wajen samarin dake zarya a wajenta ne Sunna shigowa aanguwarsu ta ringa jin hankalinta na neman tashi Bata gama jin hankalinta yana neman barin jikinta ba sai da ta ga police biyu a kofar gidansu da uncle dinta, da iyayen Aminu da Mama da Farisa Muryar mama kadai ake ji tana rizgar kuka tana fadin" Yaya a ji yaya nake rikonta? Idan ba'a godewa rikon da nake yiwa yar nan ba ai ba za'a zageni ba, Umar sharin da zaka min kennan? Dan yau kadai ka kwana ka ga bata kwana a gida ba zaka tuhumeni? Yau ta fara aka fada maka? Ai ba yau ta fara kwana a titi ba, kuma Ni nan zan shaidi kaina a kan ban san inda ta kwana ba , yaushe ma ka fara zama ba maye har da zaka dauko min police kan a duba maka y'a? Ai ga iyayen Aminu nan sun ce rabonsu da shi jiya ta yi kiransa da dare yana cin abinci ya tsallake ya tafi suma basu san inda yake ba dan sun nemi wayarsa bata shiga,, a garin Damagaran kuwa garda gardan mutane kamar su ai sun fi karfin a sace su sai dai idan abokin shashancinta ne sunna inda suke tare!" Saukar Rauda daga cikin adaidaitar tana zubawa Uncle ido da mutanen dake kofar ya saka kowa juyowa ya zuba masu ido Kallon da aka shiga masu ya saka Aminu salamar dan sahun da gagawa ya karaso ya mikawa uncle hannu bayan ya mikawa mahaifinsa sannan ya shiga bayanin abinda ya same su a jiya, cewar sun dauki sir YUSUF BELLO ne suka samu hatsarin da dole suka kwana asibiti, ya sanar masu daidai wajen da lokacin, hakan ya saka police din da ya yi aiki a jiya kuma su suka auna wajen ya ce" kwarai an yi haka, dan yanzu haka adaidaitar tana wajen mu an ce sir yace a barta a nan wai, " Bayanan da Aminu ya yi bai saka Uncle daina kallon hannun Rauda ba, dan koda ta saka kudin dake jimke a hannunta a leda ana iya gane ko menene a cikin ledar, shin daga ina ya dauketa suka dauki sir din zasu je ina suka samu hatsarin? Jaje da fatan Allah ya tsare gaba suka shiga yiwa junna bayan tafiyar yan sandan, Mama kuwa sai ya zamto magangannun da ta yi a zuciyar uncle kadai suke tsaye kikam, domin sun soke shi ainun sun kuma samu waje sun zauna daram dakam har aka watse Aminu ya masu salama kan zai je ya yi wanka ya koma police station ya ji yaya zasu kare da su kan adaidaitarsa Jiki babu karfi Rauda ta shigo falon itama bayan uncle ya shige, Mama ta bi bayansa da yarta sai itama ta shiga tana jin dari darin yannayin baban nata dan ba zata tuna ranar da ta ga fuskarsa a haka ba Hannu ya mika mata yana kallon ledar hannunta Jiki ba karfi ta karaso ta miko masa ledar tana jin wani irin nauyi yana neman lulube mata jiki da zuciya Hannunsa na rawa rawar da shaye shaye ya hadasa masa ya cira ledar ya ciro kudaden da suka saka gabansa faduwa, hakama na Mama wace ta zarro ido tana matsowa tamkar zuma da kanshi A rikice ya saki kudin, Mama ta tare tana zarro ido ta nufi dakinta da sauri ta daga gado ta cusa ta dawo wufff tana jin uncle na fadin" zaki fada min gaskiya ko kallona zaki tsaya yi ne Rauda? Daga ina kike? Wa ya baki kudin nan? Me ya miki ya baki kudin nan? Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une " Sai kawai ya silale yana dora hannayensa saman kansa hawaye suka shiga zarya a kumatunsa yana kallonta a lokacin da kirjinta ke sama sama hawaye na wanke mata fuska ya ce" kin san cewa tun jiya har yau a tsaye nake kan kafafuna? Babu inda ban je ba har gidan su Bara'atu da gidanta, tun ina gane hanya har na rasa hanyar bi, Rauda waye ya baki kudin nan har haka? Ina kika je? Ina mayafinki? " A irin wannan lokacin Rauda na cikin yannayi biyu ne, na tashin hankalin yannayin uncle dinta, da kuma wani iri gannin itace aka titsiye kan wa ya bata kudi , kuma daga ina take Mama kuwa ƙarara tashin hankalin gannin yannayin uncle ya nemi damunta har ta kasa hakuri ta tare shi da fadin" to wai me kake nufi Umur? Yaya zaka wani tisata kana son sai ta fada maka inda ta samo kuɗi?, in dai zata samo din ai da kyau zata kama min wahala da ku a gidan nan tunda kai ai hoto ne , kwarar shinkafa baka kawo mana bale cefane, ga wuta ga ruwa ga haya, ga diyar yaya ta yau da gobe, kuma kudin nan sisi ba zan baka ba dan bashi nake binta, ina dalili mutun sai kace wani na Allah , ko mema ya hannaka zuwa ka sha abinda ka saba gashi kana neman fito min da sababin sirfa? Kai walahi in dai hakane ka fi kyau a maye, gaskiya kar ka wani tambayeta inda ta samu kudi , ai tafiya ta yi kyau gobema a maimaita" Jikinsa sanyi ya karra yi ya sada kansa cike da kunnar zuciya Rauda dake hawaye ta budi baki a sanyaye ta ce" Baba, walahi babu abinda na yi, kudin nan da ka gani turo min su aka yi daga......." "Rauda ki je ki huta, zan neme ki" ya fada a harhade yana dafe kansa dake sara masa Sosai ta ji hankalinta ya karra tashi, da kyar ta iya barin wajen ta shige dakinta ta rakube tana barkewa da kukan da take ta danewa, innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, lalle ta bata ran marikinta mai kaunar ta da son gannin ta zama abin kirki a rayuwa, ya Allah da ta san fitar nan bata da wani alkhairi da bata yita ba, yanzu yaya zata dubi tsabar idannuwansa ta fada masa da Yaren bahaushe kudin da aka sako a asusunta akace ta saka kati kawai? Ta ina zata fara fahimtar da shi abinda yake tsoron nan ita RAUDA ta fi shi tsoronsa da adu'ar Allah ya sa baya cikin mummunar kadarar dake iya samunta, ita dai ta san bata kiyaye wasu abubuwan ba, ama kuma ta san har zuwa yanzu mutuncinta na tare da ita , kunci ne ya sarketa sosai, kunnayenta na jiyo mata Muryar uncle dinta da Mama sunna abu mai kama da kokowa, domin tana jin lokacin da ya rantse cewar sai ta fitar da kudin nan ya kaidawa mai su , ita kuma tace bai isa ba ai hakinta ne, tana bin Raudar kudi ne, Wannan ya karra hasala shi suka kama kokowar karfi da karfi har ya dambarata da kas ya shige dakin nata ya ringa zubar da kayan dakin yana neman kudin da kyar ya gansu karkashin katifarta dake saman gadon karfe mai runfa ya fito da su ya sameta sai ihu take wai ya ƙaryata kuma yau sai ya dauko masa motar yan sanda wai ya satar mata kudi, ga yarta zaune tana kallonsu tana tabe baki, dan ita ko a kwalar rigarta haka ya zo ya sake ficewa a gidan ya nufi inda zai ga liman domin abin nan na Mama ya masa yawa, inama ace yana da halin yin wani auren? Da ya salami matar nan ya kawo wata ko Allah zai sa ya samu mai daɗin halin da zata taya shi rike marainiyar ALLAH, a yanzu haka yana daga mata kafa ne saboda abubuwa da dama, wajen aikin nasa an kore shi dan da ya je dazu aka nuna masa dama an bashi dama ta karshe ne, dan a kulun idan aka yi albashi sai ya kusan kwana goma ba'a saka shi a ido ba, ana daga masa kafa ne saboda abokin ogan dake rokar masa alfarmar nan, zuwa yanzu kam ya gama cinye duk wata alfarmarsa ba zai ci gaba da masu aiki ba, idan har ya saketa bai riga ya riki abinda zai ringa biyan hayar da suke ciki da abincinsu ba wani halin ne zai sake saka su bayan wanda suke ciki, Si abu na biyu ba zai yiwu ba zamansa a yanzu daga shi sai Rauda da Abdul Hakim Eh lalle uncle dinta ne shi, ama rayuwa abin gudu ce, bale shi da ya ringa jin wa'azin da malan ke yi akan mashayi sai ya gama tsorata da rayuwar kanta, ga wani irin mugun bukatar ya sha dake damunsa, ji yake yi idan bai sha ba har kamar yana iya rasa numfashinsa, dan ko a jiya da ya rasa Rauda sai damuwar ta so fin karfin tunaninsa har ya fara tunanin inda zai samu abin korawar da kyar ya danni kansa ya hakura A cikin gidan kuwa Mama tamkar zarariya da kyar ya iya kama abu ta mike tana ihun a taimaketa kudinta kar ya je ya sha giya da su dukansu, fadi take yi Umar tsaya na yaga maka na shiga uku ina ya nufa? Sai dai ba shi ba alamarsa, hakan ya hadasa mata muguwar juwa da ciwon kai, a dole ya yi wani irin kwonci tsakar falon a kasa tana kukan babu mai hannata rufe Umar a garin nan in har ya taba mata kudi, babu mai hannata mayar da rayuwar Rauda ta tantiriyar ƙaruwar da ko namiji mai bin mata sai ya ji tsoron ta, dan walahi sai ta maida ita tamkar karya in dai ya yaba mata kudinta! A dole Rauda ta sake kama kanta a wurin ranar kaf, sallah kadai ke fitar da ita ta zagaya ta yi alwallah ta labe a dakinta, domin ko abinci gagarar shiga bakinta ya yi ________________________________ Cikin nutsuwa ya silala motar dake dauke da mahaifiyarsa da mahaifinsa yana jin takaicin isa irin ta Hajia, yanzu ace mahaifiyar ta yi jinya ta gama ba zata barta ta huta ba, a'a dan mulki irin na Hajia shine ta bada umarnin anna ta zo ta ga yaya jikin nata ta wartsake ne ko ciwon dama ba wani bane ta wani ja mata d'a ya yi watsi da matansa ya je yake jinyar saura, mace kulun ba lafiya sai tsomarewa take yi uwa akuyar maya Wata ajiyar zuciyar ya sake saukewa saboda gaba daya yannayin gidan nan komai ya tsufa ya lalace harda wajen parking space, ama dan bakin hali irin na Hajia da A'isha kiri kiri sun nuna gida babu abinda ya yi, shi kam yana da niya daya a kan gidan nan shine duk ranar da ya tashi ya samu isashen lokaci gidan nan sai ya saka an rushe shi sannan a tayar da gini na yayi na mamaki, ginni na sarauta ba wannan ginnin da du waje ya hade ba! "Ku shiga wajen Hajiar , ina zuwa" mahaifinsa ya fada da dan sauri ya fice a motar ya nufi bangaren matansa biyu da yayansa na wajen su Da sauri YUSUF ya kalleta ya sake bin hanyar da Mahaifinsa ya bi yana mamakin to ba yace masu na zai shiga ba su shiga su fito su maidata su je inda zasu je da shi su dawo? Ikon Allah, a dole ya fito ya budewa mahaifiyarsa ya bata hannu ta kama ta fito suka jera tana tafe a hankali cikin nutsuwa shi kuwa yana duban hanyarta kamar wani wanda ke janye da makauniya har suka zo kofar shiga ya duba ya dauki takalmanta da ta cire ya saka daga ciki inda ake ajiyewa idan an zo suka shige cikin da salama a bayane a bakin Mama, shi kuwa ya yi ciki ciki, duda ya ga yau zaman Hajiar ce kawai sai masu tayata zama, ba A'isha da ƴaƴanta da wasu cikin jikokin Hajiar na bangaren sarki da Mahaifinsa Ba laifi Hajiar ta amsa ba yabo na fallasa, ko dan ta ga YUSUF a wajen ne ko ta fara yin sanyi ne? Ita dai gatanan ama tunda ta amsa lafiya wa tambayar da Maman Yusuf ta mata cewar yaya jikinta suka ja baki suka yi shiru, Hajia na kallon YUSUF dake zaune a kasa kafar mahaifiyarsa saman cinyarsa yana amsa waya yana zuba turanci yana dan mamatsa kaffafuwan nata a hankali a hankali Kai Hajia ta dauke a zuciyarta yana ayana' yaya kike so mu shirya da ke, bayan kiri kiri kin shiga tsakanina jikana? Me na maki da zafi da kika zabi rabani da abinda na fi so a cikin zuciyata fiye da kowa? Ba zan daina gannin bakinki ba tunda bakya sona da alkhairi bakya son farin cikina' A birkice ya shigar masu baban falon gidan, wanda yake kyautata zaton a irin lokacin yana iya samun su biyun a falon koda babu yanyansu tare da su Ai kam ya same sun, su dukansu kowace na abinda ta fi kwarewa a rayuwa Bai tsaya amsa gaisuwarsu da sannu da zuwansu ba ya fuskance su yana fadin" Haka kuka zabawa kanku rayuwa ko? Ba zaku yiwa kanku wa'azi ba? Tun da jan sawayenku har shekaru sun ja kunna fama da abinda bashi da wani alkhairi a tare da ku ? Me zai rage ku ko ya cira a jikinku idan kun je kuma kun umarci yayanku su je su mata sannu? Babu wace zata ce min bata ji ba ko bata sani ba, ko dan yaronta dake dawainiya da ku ai kwa mutunta ta, shin me ya rage mana a zamanmu da ya wuce mu gyara makwoncinmu? Ace kunna nan idan ta kwonta sai dai Ni zan yi jinyarta? Kun san dai ba bari zan yi a turo mai jinyarta daga gidansu ba bayan nima inada ahali, shin me yasa ba zaku yiwa kanku fada bane a zamantakewar mu ku yiwa kanku adalci?" A tausashe ya ajiye maganarsa yana duban su ya dora da fadin" Walahi bakwa min adalci, bakwa min karra, kuma hakan ya bata min sosai" Daga wannan ya fice a falon ya yi tafiyarsa ya bar su zaune sunna bin maganarsa a zuciyarsu Hajia Rufaidah ta sake sauke ajiyar zuciya ta fara magana tana fadin" Hajia umu kin ji mijinki ko? , in ba Aban yaran nan da neman rigima ba ina hadin gabas da yama? Shi dai idan a duniya abu ya shafi matar cen bamu da damar motsa wa ko da wasa, domin kuwa cibi na iya zamto mana ƙari, kai Allah ka bamu mai son mu a aljanah" Hajia umu mai dakin tsakiya da ta fi shaka ta ce" Ko Honorable baya sauraron wa'azi a kan adalci tsakanin mataye?, sam ba ruwansa da wannan kalma sai sama sama yake wartarta idan hali ya kama, yaya za'a ce ka dube mu ka ce mana ko dan hidimar da danta ke yi da mu ma kyautata mata? Hidima ai taka ya dauka kai ubansa bai zama wajibi mu gode ba sai idan mun yi niya, kuma shi dai Honorable gaba daya bai cika kiyaye namu fushin ba mu, ai ba dole bane sai mun kula ta, idan mun yi niya ne zamu yi zumunci da ita, Ni kuwa na rantse ko mutuwa na yi kar ta zo saman gawata haka nima ko mutuwa ta yi ba zan je ba, ai wankake baya haduwa da mai dati, Honorable kuwa sai dai ya yi hakuri shi kadai ke gannin darajar rariyar da ya siya , kuma lokaci dai, zai ha ranar da zata yi masa zuba!" Hajia Rufaidah ta yi murmushin takaici tana dauke kanta tana sake tunawa wai sunna nan ya yi jinyarta? Hahahaha namiji kennan sai kace wani wanda da ace sun nuna zasu yi jinyar Tata zai amince ya barsu daga su sai ita ne?, Honorable kennan ...... ...Wannan kennan. 😍😍😍😍 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *AZAL!* 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *SAJIDA NIJAR* *PAID BOOK* _Bismillahir rahamanir-rahim._ *13* *wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nigar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍* *TALLAH, TALLAH, TALKAH* _*TOH TO TO!*_ 🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_ _Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_ Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake _Amarya_Uwar gida_ _Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_ _Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_ INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼 🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI* *🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU* _KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_ _SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_ 💁🏽‍♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻* 💁🏽‍♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI… _MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_ *ADRESSE 94536935 94.53.69.35* *Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER* KARKU BARI A BAKU LABARI🥳 Litattafan marubuciyar Duk karyar kada Yar mahaukaciya Bak'a ce Bani da zabi Daga tafia daukar soja Neman na kaina Kutkale Mage Bani da zabi Idan ka raina inda kake Umughuluk itifal Duk nisan jifa Wata kokowar Ni zan ladabi Dakika biyar Da ciwo a zuciyata Aure yakin mata Alkalamin Kadarata Dutse Daga tafiya daukar soja Makauniyace ND now *AZAL* Yana fitowa shigewa ya yi cen ciki wajen Sarki dan a dole yana so ya sanarwa wani wannan abin dan ya huce Har ga Allah ya ji haushin irin yadda matansa basu je ba basu aika yayansa su je ba Ya san ba wani zuwa da zowa tsakaninsu, ba wani gaba na hargagi suke yi tsakaninsu ba, ama basa yiwa junna maganar fatar baki tsakaninta da su, eh lalle a lokacin da suke tare an yi zama marar dadi, zaman da ba'a so, ama daga bakin lokacin da ya raba zaman ya ga ita mahaifiyar Yusuf ta zubar da komai tana rayuwarta da abinda yake gabanta, kuma a rayuwa har kyauta tanaiwa ƴaƴansu irin idan sallah ta zo din nan da sauransu, ama su bai san me yasa suke irin haka da ita ba,, idan ya yi magana sai su bashi hakuri su nuna su basuma san damuwa bane Hakan, sam baya son haka, zumuncinsu sun kashe shi karfi da yaji to me yasa suke son dan abinda ya rage su idasa murjewa? Mutun ya kwonta rashin lafiya ka kasa yi masa sannu dan muguwar akida da mugun saka kai a abu marar dadi, wannan din bashi da wani anfani! Kai tsaye ya je bangaren nasa ba tare da tunanin yana iya tarar da matansa a bangaren ba a irin wannan lokacin, ama matan nasa su biyu ne , uwar gidansa sai amaryarsa wace ga dukkan alamu itace da girki yau dan ta sha kwaliya harda ta a fada da fatar baki Da sakewar fuska suka gaisa, duda uwar gidansa kana gannin gaisuwar zaka fahimci ba har ranta take yinta ba Sunna gama gaisawar ya ce" Mai marataban yana ciki ne?" Da sauri uwar gidansa ta ce" Eh yana amsa waya ne tun dazu yace kar mu shiga shine muke jiransa, wayar nan tasa ce mai jimawa" Dan tsai ya yi dan kamar alamun kakari ya ji, sai kuma ya masu salama ya fice yana tunanin ko ya gama wayar ya shiga wani abin ne? Yana fita ta kalli amaryar rai bace ta ce" Uban waye ya sanar masa bashi da lafiya?" Da sauri, da kuma alamun kamar tsoronta take ji ta ce" Walahi babu wanda ya sanar masa Hajia, ai babuma wanda ya san bashi da lafiyar sai Ni sai ke" Baki ta tabe tana dauke kanta ta ce" Dan na san Kun aika ku fita ku yayata bashi da lafiya ku baku san baban burinsu ya kau a karagar mulkin nan su su gaje bane, idan sarki ya mutu sai kun zama abin tausayi a garin nan, dan du wannan takamar da kuke yi sai kun dawo mabarata a wajensu, dan walahi sai kin yi asarar auren dattijo da yan kannanun shekarunki, domin abinda aka zo a cin ba'a jima ana ci ba, Ni Bara na je na samo masa magani ki rufe kar ki bar kowa ya shigo nan din" Daga nan ta mike ta fice tana jin takaicin wannan ciwon ciki na sarki, ciwo ne mai gigita shi sosai, a da idan ya fara shi hankalin kowa tashi yake yi, yanzu ne take boyewa bata zama babu maganinsa dan bata son yadda ake cika masu waje ana masu ido ido, kai innalilahi ita fa idan aka bincika cikinta a yanzu haka tana cike da bakin cikin aurensa, ba dan komai ba sai dan rashin haihuwa ta so ace kannin ta aura da wannan banzan ko da yayane zai kau ya ba masu waje wajensu, gashi dai sunna zaune tamkar hoto mata hudu reras ya iya zuba yaukin fa sosai sai dai yaukin baya zama gudan jinnin da zai koma halitta! Komawa Hon ya yi bangaren Hajia ya shiga da salamarsa Hajia da Anna ne suka amsa masa a bayane YUSUF kuwa yana tsaye ne yana amsa call a lokacin Zama ya yi daf da Hajia yana tambayarta jikinta da kuma tambayarta yaushe zasu koma a cire abinda aka daure karayar ita kuma tana bashi amsa da kular itama, domin danta kam tana son abinta, abinda suka aikata shi da mahaifiyar Yusuf ta dauki hakan a matsayin ya hadu da muguwar budurwa ne ta kai shi ta baro shi kuma ta yafe masa ama ta kasa yafewa y'ar da aka karbi budurcinta aka rabata da iyayenta, aka soki zuciyar iyayenta aka katse mata karatunta aka wulakantata a idannuwan abokai da dangi, Hajia kennan Yana gama wayar ya dube su ya ce" Mu je Mah, daga cen zan je park ne yau ban je ba" Mahaifinsa ne ya fara mikewa da kula ya ce" Karbi ky din yanzuma kai zaka tukamu da ka ajiye a kusa da Mamanka ka san ba zan barta tuki ba ko?" Murmushi Maman Yusuf ta yi ta dauki Ky din dan a bayane Hajia take kallon mahaifin Yusuf da mamakin yau ya masa magana a tausashe, sai dai kuma farin cikin hakan ta ji, domin ita dama bata da damuwa da soyayarsa da d'ansa Salama mama ta yiwa Hajia gannin ta yi kiran Yusuf , shi kuwa a dole ya je ya tsaya gannin mahaifinsa tsaye yana kallonsa A tausashe Hajia ta ce" Dama dan na roke ka ne idan ba damuwa ka kai Ni gannin likitan ranar Litinin in sha Allah?" Zubawa fuskarta ido ya yi sai kuma ya kalli mahaifinsa Ajiyar zuciya ya sauke ya ce" Zan duba na gani in sha Allah" Daga haka ya wuce shima ya bar mahaifinsa na sake yi mata sai da safe dan yauma ba zai kwana a nan din ba, kuma ba zai kwana gidan maman Yusuf ba dan ba kwananta bane, fushi yake da matansa biyu kuma sai an bashi hakuri koda zai hakura Yana fitowa ya samu Yusuf a tsaye yana duban agogo, magariba ce ta shigo dan suka nufi masalaci bayan sun sanarwa maman Yusuf din dake cikin mota tana kallo a wayarta hakan ya sa itama ta fito ta koma ciki dan yin sallar Sunna gamawa suka shiga motar Yusuf ke ja Abu na waya da Aminu yana fada masa daidai inda zasu tsaya yana daidai wajen Sunna karasowa wajen suka dauki Yusuf sai godiya yake yiwa su Mama kan adaidaitar da Yusuf ya sa ya je ya amsa sabuwa dal da ita harda karin kudin awo, sai fatan alkhairi yake yana fadin lalle Yusuf din sarki ne kuma uban talakawa Shi dai tukinsa yake yi yana jin dan feeling na abinda ya kwana biyu bai yi ba, rabonsa da nanikar jikin wata kwana biyu fa cirrrr, kuma har mantawa yake yi saboda rashin lafiyar mamansa, ama yau sai yake jin wani feeling na neman damunsa A nutse suka karasa cikin anguwar har kofar gidan Sunna tsayawa Aminu ya nuna masu gidan yana faɗin " Ga gidan nan sir, ama inaga shi uncle din nata baya gidan dan yanzu a masalaci liman na fada min ko na ganshi? Yace sau biyu tana zuwa nemansa wai tunda ya fita dazu ransa a bace" Honorable ne ya dube shi da kula ya ce" Ransa a bace? Kwananta a wani wajen ya saka ransa bacewa ko ina iyayenta ne ko hutu ya zo wajen uncle din nata?" A hankali Yusuf ya jinginar da bayansa jikin kujerar motar yana sauke dubansa daga kan Mahaifiyarsa dake kallonsu yana jin Aminu na maimaitawa Honorable cewar RAUDA marainiya ce gaba da baya a hannun uncle din nata take Shiru wajen ya dauka, na tarin alhinin jin maganar ne ko mene? A sanyaye Mah ta sauko kafarta daga cikin motar bayan ta bude ta ajiye wayarta baba tana fadin" Bari Ni na shiga ka ga idan yana nan din sai ya maku iso" Haka kawai ta ji zuciyarta ta buga mata jin labarin yarinyar, sai ta ji bari ta shiga ko sa ga marikinta su sanar masa ga asalin inda ta kwana ta yiwu da akace ya fita hankalinsa tashe ya daina fushi ya yi hakuri Da ido YUSUF ya bita har ta bude karamar kofar gidan ta shiga sannan ya dawo da dubansa kan Aminu dake dan yiwa Ana shinfidar wasu daga cikin abinda Rauda ke ganni a gidan rikon nata Salama Maman Yusuf ke yi tana karawa, ama ba amsa, sai murya dake tashi sama sama da alwashi kala kala wanda ya sakata dakatawa a dole tana tunanin ta koma ne ko ta shiga? Ta daga kafa da nufin shigewa ciki ta ji sama sama murya na fadin" Rauda idan har ubanki ya shanye giya da kudina nice ajalinsa, kuma kema nice ajalinki ki rubuta ki ajiye, munafuka algunguma, ki bani kudina nace , ki tashi du gidan ubanda kika san zaki je ki samo min kudina ki je ki samo idan ba haka ba na wulakanta ki na je na dauko dayan shegen na yanka shi!" Hankalin Mah ne ya mugun tashi, da sauri ta juya har tana jin kafarta zata tashi na ciwo ta fito ta nufo mota tana haki Da sauri YUSUF ya bude motar ya fito ya kamo hannayenta yana kallon yadda take haki hankalinta tashe, Abu ma dake tsaye shi da Aminu gefe sun nitsa a labarin Rauda da sauri ya karaso yana kamota ba wata wata ya rungumeta a jikinsa yana fadin" Hey Madame, menene, me ya faru?" Hankali tashe har hannayenta na rawa ta fadi abinda ta ji da ta shiga, da sauri ta ce" Wacece RAUDA? Inace wajen yarinyar da muka zo ne , me ta yiwa Mamanta take fadin kalaman nan a kanta innalilahi Wa inna ilaihi raj'une" A nutse ya mayar da hannunsa ya rufe motar ya juyo yana kallon mahaifinsa dake faman fada mata kar ta daga hankalinta ba komai bane bari ya shiga ya gani A tausashe ya ce" Aba bari na shiga na gani" Yana fada ya juya ya nufi hanyar shiga, da sauri Aminu ya biyo shi yana fadin" Biya Muradi da zaka yi hakuri na tabo wata mace ta shiga, ka san matar nan da sharin tsiya, gashi bata gannin girman kowa kar ta lika maka wani sharin a banza a wofi" Murmushi YUSUF ya yi masa ya nausa kansa ciki yana salamar da ta zame masa jiki ciki ciki Yana shigowa Farisa ga fito daga bayi ta gama aikata kashinta na magariba da ya zame mata jiki suka yi ido hudu Ido ta zuba masa kafin da sauri ta dubi kafarta dake dauke da dati harda zannin jikinta, zannin da ta wuni da shi shekaran jiya da jiya ne , yau fa har zata cenza tace bari dai ya karra kwana biyu sai ta cenza dan bata kayanma ai ba kyau,sai gashi an yi rantsatsen bako? Da sauri ta wuce shi ta yi cikin gidan har kamar zata kifa Tana shiga ta ce" Mama, wa bilahilazi Balarabe a cikin gidanmu, Allah ka sa bakona ne , Allah Allah Farisa Allah amen" Uwar dake daure da zani saman munafata ta dubeta itama yau din dai wankan nan bata yi shi ba, ta wuni a daki ko abinci bata ci ba ta ce" Balarabe kuma?, Farisa zan ci uban ubanki idan har baki daina kawo min shirme a yau ba, me zai kawo Balarabe anguwar nan dan ubanki?, ko wajen wannan ya zo ai ba zai shigo min gida ba ko?" Da sauri ta tari uwar tana fadin" Allah ya sawaka ya zo wajenta ki ji kai mugun fata , kina ji ina adu'ar Allah ya sa wajena ya zo ki wani ce wajenta, ke Rauda gaskiya tashi ki shiga ciki kar ya ganki ki masa asirin da kika saba da munafukan idannuwan nan naki, Ni dai kuma kar ku bari ya gane ana neman baba Umaru gaskiya kar ku zubar min da mutincina!" Magana take yi tamkar ta sako da sako, magana take yi ta rashin mutunci tana hantarar uwar da Raudar baki daya domin du ta gigice Mikewa Rauda ta yi idannuwanta ko gannin kirki basa yi Sama hijab ne a jikinta mai ruwan anta har kasa ama bashi da hannu ya dai kama fuskarta das ya fitar da zagayen fuskar nata, hakan ya sa fuskar ta fito fayau da ita sai lebenta da ya dan bushe da kuma idannuwanta da suka kara nutsewa suka yi luhu luhu Niyarta ta sake komawa masalaci daga nan kuma ta nufi gidan giyar da yake zuwa, in dai yana cen shikenan sai ta dawo ta nutsu ta kuma ci gaba da yi masa addu'a, dan jikinta na bata mugun abin da ya ringa bata a ranar da zata iya kiran ranar da Azal ta fadawa ahalinta Da sauri Farisa ta riko hijab din tana fadin" Rauda nace kar ki fita fa!" Da kyar ta iya yiwa idannuwanta luuuuuuu ta bude bakinta ta fara magana ta ga an daga labule an shigo ama bata ga mai shigowar ba, a hargitse ta ce" Idan kika kuma taba min sutura da kazantar nan taki sai na karya maki hannu, idan kika kuma daga mun murya sai na janyo makogwaronki FARISA!" Da sauri ta yi baya tana neman yin kusa da mamanta, dan ita ta sha'afa kan Wacece RAUDA ita kuma Mama tunda ta ga wanda ya shigo sai itama ta shiga kunce hijabin dake daure a kugunta tana kokarin sakin fuska ta ce" Barka da zuwa baki muka yi ne?" A hankali Rauda ta juyo da niyar zagayesu ta fice idannuwanta suka sauka a kan fuskarsa ya zuba mata ido shima sannan ya dauke ya sake kallon hoton dake dakin daya kwal wanda kwarai ya san fuskar mutumen, ama a inda ya san mutumen a waje ne marar kyau, wajen da su mutanen suke kwalewa shi kuwa yakan je ne dan ya yi nasa kalar kwalewar shima "Ba wajenki na zo ba" YUSUF ya fada a hade yana kaucewa daga nufo shin da Mama ta yi da kujera A hade ya ce" Ke ?, menene ?" Rauda dake tsaye bayan ta dauke kanta tana tunanin me kuma ya kawo wannan gidansu ta dago yana kallonsa Kwarai da ita yake, Ke ? Menene? Eh lalle da ita yake , sai ta ji ba zata iya amsa shi ba ta sake dauke kanta da nufin ficewarta ta tafi suka ringa jiyo salama daga bakin kofa ta muryoyi masu dan yawa kuma maza ne Gaban Rauda ne ya yanke ya fadi, daga tsayen da take sai ta matsa sosai ta yi ciki kadan dan ana amsawa masu salamar salamarsu ne Mama na fadin" To wai kuma su waye da daren nan Ni yau sai bakin mutane ke zuwar min!" A tausashe Liman ya ce" Ba baki bane maman yara, su liman ne" Itama sai ta samu kanta da yin tsittt kafin ta taho jiki ba kwari tana jin zuciyarta na dokawa jin su liman ne, su liman? Idan tana da tunani ba zata tuna yaushe liman ya taba sako ƙafarsa gidan nan ba, haka kuma ita dai ko a hanya ba abokin gaisawarta bane bale tace sunna gaisawa Abu daya ta yi tunani an zo ne a mata nasiha da Umar dan kamar ai ana haka a anguwar sukan je dan wani tsirku su yiwa mace da mijinta nasiha ta rainin hankali, namijin dake zaune da matarsa bai isa ya mata nasiha ba sai sun je da wasu wandunansu tsalau tsalau wai sun zo nasiha Tana fitowa bayan YUSUF ya fito ya ga harda iyayensa a yan shigowar da sauran mutanen da bai san su ba ama suma sunna ganninsa da mutuntawa sosai suka bashi hannu suka gaisa da daraja junna sai kuma ya ga fuskar mahaifiyarsa tamkar wace ta jike da hawaye nan take ya ji tamkar hankalinsa zai tashi, ama kuma ya yi iya yinsa ya dane yana kallon kowa ciki harda Rauda da ta fito da tabarma jin ana fadin a kawo tabarma, jikinta na rawa ta shinfida masu ta tsuguna tana bin ledar dake hannun Liman da kallo gabanta na ci gaba da faduwa A tausashe Liman ya ce" Ina fatan na same ku lafiya, sannan ina baku hakurin zuwan da na yi maku a irin wannan lokacin" Shiru ya yi yana neman dukan hanyar da ta dace ya sanar da abin dan shima hankalinsa a tashe yake sosai A hankali ya ce" Wunin yau mun fita da malamai, sai da yama da na zo aka shaida min mai gidan nan ya je nemana sau biyu bai sameni ba, sai kuma RAUDA da ta je ita dinma sau biyu nemansa baya tare da Ni, a lokacin gannin yama ta shigo magariba ta kusa sai na yi adu'ar Allah ya sa lafiya kuma Allah ya kawo shi masalaci sai mu gana, to bayan an yi sallar magaribar muna zaune da su malan da datijawan anguwa a bakin masallacin muna karatu kamar yadda muka saba wani mashin ya tsaya zo da gudu aka wurgo mana wannan ledar aka wuce dan ko tsayawa mashin din bai yi ba bale mu tantance mai shi da kuma kalarshi mun dai san baki ne kuma masu tuka shi da shigar baki a jikinsu har fuskarsu" Ledar da ya nuna kowa ya zubawa ido, ciki harda Rauda da Mama wa'inda hankalinsu ya fi tashi, domin kar ku manta duk rigimar mama da uncle tana son mijinta, irin matan nan ne masu mugun halin da duk wani wanda ya rabe su ba zai ji dadin zama da su ba A sanyaye Liman ya ce" A dole muka bude ledar bayan an tabbatar da ba bom bace, mun ga sutura ta namiji ba kyan gani da waya yar karama, a lokacin aka yi kiran mu aka sanar mana kayan ko na waye kuma akace mu saurari kira, abinda dai muke zato ta yiwu yan garkuwa da mutane ne ko wasu wa'inda rikicin su ya hado su da shi, fatan da muke yi Allah ya sa lafiyarsa kalau " A rikice Mama ta rarafa ta warto ledar, duk irin yadda aka ringa kokarin hannata budewa ta farke ledar ta zarro rigar uncle caba caba da jinni, da wandonsa sai wayar nan ita dinma duk abin jinnin ya bata ta A haukace ta saka ihu hadi da sake daga Kayan, Rauda kuwa da zuciyarta ta yi bugawa daya tak tana mikewa dan karasowa ta gani kaffafuwanta suka dauketa suka yumata da kas A rikice mahaifiyar Yusuf ta janye hannunta daga cikin nasa ta ririko Rauda jikinta, dan wasu sun nufi mama ne wasu sun nufo Raudar ama ba damar su masu rikon da Mace zata iya yi masu Idannuwan Rauda luuuuu suke yi numfashinta na yin sama sama, A hankali ta wani irin nisa dan neman sakin kuka, sai dai ba kukan sai nishin dake fita mai haɗe da zazafan numfashi A birkice da kyar ta ce" Ya mutun shima? Haukacewa zan yi, in har ban mutun ba nima haukacewa zan yi, ya mutun ko? Shi dinma an kashe shi? Ya mutu ko? Shikenan sai Ni sai ita? Haukacewa zan yi kwakwaluwana juyewa zata yi, haukacew zan................." Dif maganarta ta dauke , gaba daya jikinta ya saki, kanta a kirjin mama ta saki rikon da ta yiwa lafayar maman ta summe Da sauri YUSUF dake tsaye kikam yana kallonta ya duko ya tare Mama da ta fashe da wani irin kuka Hankali tashe ya ce" 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *AZAL!* 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *SAJIDA NIJAR* *PAID BOOK* _Bismillahir rahamanir-rahim._ *14* *wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nigar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍* *TALLAH, TALLAH, TALKAH* _*TOH TO TO!*_ 🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_ _Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_ Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake _Amarya_Uwar gida_ _Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_ _Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_ INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼 🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI* *🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU* _KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_ _SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_ 💁🏽‍♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻* 💁🏽‍♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI… _MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_ *ADRESSE 94536935 94.53.69.35* *Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER* KARKU BARI A BAKU LABARI🥳 Litattafan marubuciyar Duk karyar kada Yar mahaukaciya Bak'a ce Bani da zabi Daga tafia daukar soja Neman na kaina Kutkale Mage Bani da zabi Idan ka raina inda kake Umughuluk itifal Duk nisan jifa Wata kokowar Ni zan ladabi Dakika biyar Da ciwo a zuciyata Aure yakin mata Alkalamin Kadarata Dutse Daga tafiya daukar soja Makauniyace ND now *AZAL* A rikice ya ce" Dan Allah, kar ki yi, kar ki zubar da hawayenki kuma i beg You mama" Hannayensa ta jimke kirjinta na bugawa tana kukanta kunnayenta na jiyo mata salalamin su Liman dake fadawa Mama ta daina mana ba fa mutuwa ya yi ba dan sun ce zasu kira, kuma basu je wajen yan sanda direct bane dan dole su fara sanar masu, in sha Allah za'a ganshi kar su daga hankalinsu mana, gashi Rauda har ta summa dan Allah a daukota a kaita asibiti A rikice Mama dake kuka tamkar zata zauce ta ce" Idan da mutun a nan kuwa sun fitar da shi a hayacinsa, ku duba ku ga yadda jinni ke zuba daga jikin rigarsa harda guda guda? Wayo allahna Umar, muna zamanmu ka fita da kudi , shin da barayi ka hadu ko me? Wayo allahna ya tafi ya BARNI da duniyar da ya'ya, Umar dama da wuri zaka mutu ka barni? Yauma muna rikici ya fita, da kudin da wancen tsinaniyar ta kawo ya fita dan na amsa ya amshe ya fita da su, ko dai a gidan giyar aka kashe shi? A ina suka kashe min shi?" Su liman kam sai suka koma yan kallo, domin su dai ba ririketa zasu yi su rufe mata baki ba, kuma babu mai hurumin yi mata tsawar ta kamawa mutane baki su kam an ce za'a yi kiransu hakan na nufin da wahala idan Umar din ya rasu, ama sai wasu abubuwa take yi kamar ba musulma ba? Ga furucin bakinta ya yi tsauri da yawa Mikewar YUSUF da Rauda a hannunsa sukutum ya saka su liman din kallonsa Ba da wani tsaye tsaye ba ya ce" Asibitin za'a kai ita wannan din" Daga haka ya yi gaba mama na biye da shi da sauri, abansa kuwa ya karra tsayawa suka sake yin bayani da su Liman A lokacin da mahaifinsa ke neman fitowa Mama na binsa tana faman taro zani ta biyo shi har wajen motar ta kama abin motar hakan ya sa ya dakata bai wani kureta da kallo ba ya ce" Lafiya?" A birkice ta ce" Iyi? A'a na ga kun dauketa zaku je da ita, ai summa ce kawai ba wani abun ba, idan kuwa da ita zaku je mu je tana farkawa mu juyo saboda kar su yi kiran bata nan, ka ga in kuɗi suka yanke sai ta kawo masu abinsu su bani mijina" Bai taba tunanin zai iya haduwa da dan adam mai irin halayyar nan a nan kusa kusa a garin nan ba sai yau da Allah ya hada shi da ita, ya rasa mai zai yi tunani ko yace a kanta, ama ya fi ajiyewa ransa cewar bata da hankali ne matar nan Kasancewar bashi da wani hadi da ita, kuma a tsayen nan dai itace kawai yar uwar yarinyar da suka dauka, duda liman din kansa ya bada amanar a tafi da yarinyar zasu zo suma sai ya dan sake cewa" Ki yi hakuri ki koma, ai zata dawo idan ta warware, Allah ya bayyana shi" Ya juya ya bude motar ya shiga ya ga still ta kama abin motar ta bude A haukace YUSUF ya kalleta ya ce" Ke, rufe min mota!" A birkice ta saki motar tana ja baya tana bin motar da kallo domin tana rufewa ya tayar da motar ya yi gaba A wajen ta durkushe cikin shiga uku da neman zaucewar tunani ta shiga kama sunayen Umar din da Rauda tana faman sambatu tamkar wace ta haukace, mutanen anguwa kuwa saboda Umar din da ita Raudar suka ringa yi mata sannu da adu'ar Allah ya bayyana shi, ama babu wanda yace ta tashi daga inda take bale ace ta je ta suturta jikinta da kyau ta dauki carbi kan Allah ya sanyaya masu abinda ya tunkaro su Sai da ta gaji dan kanta ta mike ta nufi cikin gidan tana hada hanya Tana shiga kunnayenta suka jiyo mata kida na tashi sama sama a yar karamar redionta Har ga Allah sai da gabanta ya fadi, dan bata tunanin a kusa kusan nan akoy wanda zai saka mata kida a gida bayan abinda ya faru Da sanyi sanyi ta karasa falon, nan ta samu Farisa ta dage sai dirkar rawa take yi hannaye a kugu ta juya nan ta juya cen tana bin wakar gwomja ta warrrr Idannuwa ta zubawa Farisar kafin ta karasa ta dauki redion ta rotsa da kasa rai bace ta ce" Ke kina cikin hayacinki kuwa? Dan ubanki ubanki ne aka kawo kayansa da jinni kaca kaca ke kuwa kike rawa kina juyi bayan ba'a san a wani hali yake ciki ba?" Galala Farisa ta yi itama da mamakin uwar Tata a fuskarta ta ce" Mama inace yanzu kika cewa kece ajalinsa dama, to dan an kawo maki cewar ya mutu ba shikenan ba?" Mama sai da ta ji tamkar an dauki abu an datse kafafuwanta, saboda da gasken gaske mujirya ta kama kaffafuwanta ta nemi bugata da kasa daga tsayen da take A rikice ta ce" Farisa fada nake yi dan ya daukar min kudi, ama ke kin san ina son babanki ko " Farisa ya tabe baki ta bi bayan redion da aka rotsa ta dauke ta yi dakin Rauda da ita, dan tana so ta je ta dan bincika da wuri wuri ko ta samu na samu ta dan adana gefe kafin Raudar ta dawo, fatanta Allah ya sa ta bar wayarta da kuma jakar kudinta, kai da itama ta kile dan walahi tana ji tana gani zata ce itama saurayinta ya kawo mata iphone din, ai ba ita kadai take da damar yin saurayin ba dan wulakanci! Tuki ne ya yi mai gaggawa, hankalinsa a kan Mahaifiyarsa dake ambaton sunnan yarinyar da yanzu yanzu ne ta ji sunnan ama kamar wata wace ta saka mata shi da kanta Sunna karasowa ya fito dan sake daukan yarinyar ya kaita ciki kafin ma a kawo kujerar dora marar lafiya ko gadon, sai ya ga Mah ta cire mata hijabi ta cire mata ribom sai faman son tahsinta take yi tana jimke da hannunta da dayan hannun kuwa tana dan shafa gefen fuskarta a hankali tana fadin ta farka mana Kansa ya dauke a kanta ya ja gefe har aka zo aka kamawa Mah aka dora yarinyar aka fita da ita aka yi ciki da ita Wurin zama Mah ta samu ta zauna tana dafe kanta da hannayenta bibiyu A nutse ya karaso ya duka gabanta ya saka nasa hannayen yana cire nata yana kallonta ya ce" kamar kin saka damuwar wace bakima sani ba da yawa a ranki Mama, Please ki sanyaya ba komai fa, zata farka ne yanzu sai mu maidata gidansu mu je gida ki huta" Bayan zuba masa ido da ta yi sai ta samu kanta da cewa" Mu maidata? YUSUF mu maidata fa ka ce?" Idannuwa ya zuba mata yana son gane me kennan A sanyaye sosai Mah ta ce" matar da muka bari a gidan cen sam bata cencenci rikon yaro ba, ko nata ba zata iya ba tarbiyya ba bale wannan da take kishi da ita, Yusuf cewa fa take yi wai idan bai dawo ya kawo mata kudinta ba itace ajalinsa kuma itace ajalin yarinyar nan , Ni ban san tsakaninsu ba, ban san me ta yi mata da zafi har ta tsaneta haka ba, ban kuma san ko inada hurumin shiga wannan rigimar ba, abu daya na sani shine daga nan yarinyar nan zata je ne gidana kuma a gobe gobe zan shigar da karra dan kar matar ta rigayeni, Yusuf ai dadinta muna da sarakai masu adalci da hukuma tsayayiya, kuma a yannayin yarinyar cen ta yi shekarun da ta isa zabarwa kanta inda take son zama, Ni dai ina ji a raina kamar taimako ne zan yi, kuma kamar idan na yin Allah zai dubeni da idon rahama nima ya yafe min kura kuraina " Idannuwansa ya lumshe a hankali , bai saki hannunta ba a sanyaye ya dora gefen fuskarsa a tafukan hannayenta yana jin dumin hannunta yana aukawa a tunani Lokuta da dama idan ya zauna da mahaifiyarsa sai ya ji zuciyarsa tana girgiza , hankalinsa na tashi da nasa shima laifin Mahaifiyarsa bata taba daina neman afuwar Ubangiji ba kan abu daya tal da ta aikata wanda bayan aikatashin ta rike abinta har ta haifi abinta kuma ta so ta raini abinta Allah ya amshi abinsa Ama a haka a kulun idan ta budi baki zaka ji tana tsoron haduwarta da mai sama kan wannan abu, to ina ga shi jama'a? Ya mayar da mace abin shigarsa dan samun nutsuwa Yana yi yana hawayen bakin ciki da tashin hankali Bai rasa abin ajiye hudu idan yana ra'ayi ba, ama ya kasa tsayawa waje daya bale ya ajiye din, ya yi nan ya yi cen da ransa Kwarai shi din ya kasance mai aikata aiki mai munin gaske, wanda idan ta ji wa'azi wani lokacin yakan kasa rintsawa A hankali ya sauke ajiyar zuciya ya dago idannuwansa yana kallon mahaifiyarsa A ransa yake aiyana 'ni kuwa zan tsaya maki har sai kin kai ga cikar burinki dan samun nutsuwar zuciyarki Mah ' "Sir, ta farka, ama ta ki tsayawa mu mata allurar barci duba da bugun zuciyarta ya yi yawa ko ma samu ya dan daidaita mu yi mata gwaje gwajen da ya dace dan mu dorata kan traitment" Mikewa ya yi , Mama ta bi bayansa suka nufi dakin Budewa ya yi ama ya ki shiga sai Mama ce ta shiga sannan ya bi bayanta ya tsaya yana kallon Mama Gadon Mama ta karasa da sauri ta zauna ta dago kan Rauda ta janyota ta rungumeta a jikinta da dan karfin da ya saka Rauda dawowa duniyar mutane har ta dan saurara daga rizgar kukan da take yi hancinta na shakar sansanyan turaran ruwan mama kunnayenta suka shiga jiyo mata kalamai a sanyaye kamar haka" me yasa zaki rikita kanki har haka ne? Kina son kamuwa da wata cutar ne? Waye ya fada maki ya rasu ne? Da ace sun kashe shi da wahala su kawo wayar nan, ina mai kyautata zaton yana raye sun yi haka ne dan su rikita mutane ya zamo da zarar sun yanke kudin da suke so a basu dan a amshe shi, kuma kin ga Honorable ya amshi wayar yanzu haka da ya ajiye mu ya tafi wajen commisiona na police dan ya masa maganar, Haba Rauda sai kace ba musulma ba? Koda rasuwar ya yi sai ki kasa yin tawakali ne? Allah baya barin wani dan wani ya ji dadi RAUDA, idan har Allah ya so zai dauke maki kowa ne ya barki ke kadai, saboda wannan sai ki kashe kanki kema? Hana Rauda ki yi hakuri kin ji?" Tamkar wace Mama ta tuno mata da wani gibi, ko kuwa kalmar hakurin daga bakin uwa ne bata saba ji ba ta ji a yau? Ko rungumeta a rarasheta ne bata saba samu ba? Abin dai ya shige mata zuciya har ya saka ta dago idannuwanta ta zubawa fuskar Mama mai dauke da ni'ima da haske mai daraja kallo kafin a hankali ta fashe da kuka tana saka hannayenta a hankali ta rike na Mama ta kai kanta a hankali ta ɗora saman kirjin Maman tana sake riƙe maman tana kuka irin na cikin makogwaron nan mai zafi da ratsa zuciya muryarta na sarkewa ta ce" Dama iyayena da kanaina sun rasu, shine kawai gareni sai Abdul, shine kawai gareni , su ne kawai dalilin da yasa nake tafe da karfina, idan na rasa su Ni na san Bani da karfin dazan iya jurewa, innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, dan Allah Hajia ku taimakeni a samo min Abanmu, ko nawa suka yanka min zan biya su bani shi, ki nawa suke so zan basu Ni dai su bani shi" Mama, tausayi, tashin hankali, mamaki duka sun hadu sun rufe mata zuciya, haba koda ta ji ta san wannan kam da wahala idan ta haɗa jinninda yarinyar irin yadda ta ringa jaza mata alkaba'i, haka kuma jin iyayen yarinyar duka sun rasu sai ya sake daga mata hankali, uwa uba kuma jin wai ko nawa ake so zata bada, aikin me take ne? Shigowar docter da baban file a hannunta ya saka Mama bada hankalinta wajen docter, har zuwa lokacin kan Rauda a kirjinta tana dan dadabata a hankali, Yusuf kuwa yana tsaye ne yana sauraronsu " wannan ba itace aka kawo jiya ba? " Docter ta tambaya Mama ta tabbatar mata itace Docter ya fita , jim kadan ya dawo tana sake bude takardar hannunta ta ce" To ai a jiya duka abinda ya dace na gwaji mun mata, sai dai idan kunna da bukatar a sake wasu to, dan jiya sir yace a mata komai dan lafiyarta" Murya a shake sosai Rauda ta ce" Lafiyana kalau, gida nake so na je, Lafiyana kalau " Mama ta dago daga kallonta ta kalli YUSUF dake tsaye bai ce masu komai ba, a tausashe ta ce" Eh yanzunma summa ne ta yi shi yasa muka dawo saboda wani abu da ya daga mata hankali, idan ba damuwa sai mu juya gida ?" Likitar ta karaso ta fitar da abubuwan aune aunenta ta shiga auna RAUDA, wace lebenta ya yi Jajajir, hakama saman hancinta da wajen idannuwanta du sun kumbure sosai hakan ya sa da kyar take daga idannuwan , leben kuwa sai haske yake yi na abin kukan da ta ci Da kula sosai likitar ta ce" kunna iya tafiya Madame, ama a sayi wannan maganin ta ringa shan daya idan zata kwonta na tsayin sati guda saboda bugawar zuciyar nan, kuma ta yi kokari ta cire damuwar dan yawan yanke jiki a fadin nan daga nan ake haduwa da mugun hawan jinni mai naci, Allah ya bada lafiya" Daga nan ta yi gaba da kayan aikinta a hannunta Mama ta dubi Rauda bayan ta dago kanta a tausashe ta ce" Kin ji abinda likita tace ko? Ki daina kukan hakanan, mu je gida ki huta za'a ganshi kin ji?" Shi kam mamakin mama ya fi komai damunsa, su mata me yasa suke da saurin sabo? Haka kawai daga gannin yarinyar sai rungumeta take yi tana faman neman dagawa mutane hankali a kanta? Kai shi kam bai san me zai ce ba kam, ama Mama akoy rigima Allah kuwa, meye hadinta da wannan ne? Shi ba abinda ya bashi haushi sai jadadawa da take yi wai ko a je ko nawa ne zata biya? Shin aikin uban me yarinyar take yi da bata jin kunyar kowama ya ji? Kai subahanallah ashe rashin jin maganar mace haka yake da kayan haushi? Shi haushima take bashi kamar ya buge mata baki yake ji idan tace din nan ko nawa ne zata biya, aikin banza aikin wofi yarinya tunda ya santa cikin kaya kaya take? Shirme kawai! Da kyar mama ta iya ganar da ita dalilinta na ta bita, sai da ta nuna mata ta ji furucin maman Farisa sannan ta yi gumm ta kasa cewa komai, sai alfarmar da ta nema kan zata je wajen kanninta gobe? Mamah kuwa ta nuna mata zata kaita ne da kanta dan haka ta samu yin shiru ta koma kukan zuci da addu'a ga wayarta a kirjinta wajen da za'a kaita kawai take jiran gani dan ta samu ta yi kira, ba zata iya rintsawa ba in har bata san inda uncle dinta yake ba, kuma ta san idan ta fadawa mutumen ta zai taso ko me yake yi ya zo ya nema mata shi, kuma ko nawa zasu yanka masa zai biya ne dan ta samu nutsuwa da kwonciyar hankali...... A lokacin da YUSUF ke tuki har ya dauki hanyar gidan Mama kira ya shigo wayarsa na Mahaifinsa Dan rage tafiyar ya yi dan a tunaninsa ko ya zo asibitin ne bai gansu ba? Dan ya sanar masa sun taho gidan Mama Yana dauka ya saurara yana jin Muryar mahaifinsa yana fadin" Yusuf, ka ganni na zo fada , ina tare da commitiona aka yi kirana cewar sarki ba lafiya, Hajia ce ta yi kiran nawa wai ba dama, shine na zo ka ganmu nan ance ba za'a kai shi asibiti ba, ama ana tsaye kansa ga likitoci nan, Ni ina ta lafiyarsa ne Hajia tace wai na yi kiranka in me kake yi, in a ina kake ka je maboyarka ku zauna har Allah ya tashe shi" Tsai ya yi yana sauraron maganar ,. Maboya? Shi walahi ya manta cewar akoy maboya da aka masa wace abin ya bashi dariya a lokacin da akace a dukkan lokacin da wani abu ya taso ya je cen Waje ne wanda zuwansama hatsari ne a yanzu dan dare ya shigo Gashi sun ce idan suka ambata masa ya saki hanya kar ya bi cikin gari Ikon Allah me kennan? A tausashe ya ce" Abu, me ya hadani da wata maboya dan Allah? Gamu fa zamu je gidan Mah ne " Mahaifinsa dake tsaye shi da Hajia wace ke zaune tana kallonsa ta masa alamun ya tirsasa shi, dan haka ya ce" Sako zuwa gare ku masoya kuma mabiya wannan littafi nawa mai taken AZAL *In sha Allah da zarar na gama free page zamu koma posting a telegram ne, dan haka wa'inda suka saye shi su yi kokarin sauke telegram, telegram, zamuna yin posting dinmu a cen ne, na gode* 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *AZAL!* 🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶 *SAJIDA NIJAR* *PAID BOOK* _Bismillahir rahamanir-rahim._ *15* *wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nigar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍* *TALLAH, TALLAH, TALKAH* _*TOH TO TO!*_ 🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_ _Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_ Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake _Amarya_Uwar gida_ _Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_ _Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_ INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼 🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI* *🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU* _KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_ _SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_ 💁🏽‍♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻* 💁🏽‍♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI… _MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_ *ADRESSE 94536935 94.53.69.35* *Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER* KARKU BARI A BAKU LABARI🥳 Litattafan marubuciyar Duk karyar kada Yar mahaukaciya Bak'a ce Bani da zabi Daga tafia daukar soja Neman na kaina Kutkale Mage Bani da zabi Idan ka raina inda kake Umughuluk itifal Duk nisan jifa Wata kokowar Ni zan ladabi Dakika biyar Da ciwo a zuciyata Aure yakin mata Alkalamin Kadarata Dutse Daga tafiya daukar soja Makauniyace ND now *AZAL* Mahaifinsa dake tsaye shi da Hajia ta masa alamun ya tirsasa shi, dan haka da yannayin nada umarni ya ce" Ka san idan akace ka je da dalili, ka je din sai na bukaci ka fito ka fahimta?" Dan jim ya yi kafin ya bashi amsa da to Hanyar ya dauka cikin tuki mai gagawa da kula, yana tafe yana kiran wa'inda ke ba wajen tsaro ya sanar masu shine zai shigo layin har ya karasa layin gidan da aka yi a cikin jeji wanda zaka dauka wani waje ne daban aka ware a cikin gari aka dankara wannan fasali da tsari na tsaro a wajen Yana shigowa wasu maza hudu suka saka motar a tsakiya yana tukin a hankali su kuwa sunna biye da motar da gudu da kaffafuwansu har wajen get din gidan wanda aka yi shi tamkar garun gidan, dan in dai ba Sannin wajen ka yi ba ba zaka taba gane ga get din nan ba, domin a saje yake sosai da gidan kuma tsayin kofar a hade take da wani abu da aka saka da cen kasa ya hade da kasa, babu yar hudar da zata shaida maka ga wajen da zaka bude ka shiga sai masu tsaronta da suka san cikinta da wajenta Da gagawa wasun dake kofar suka bude kofar wadinnan na ja gabar tafiyar, sunna shiga wasu hudun ne suka sake raba motar biyu gaba biyu baya ya zamo hudu gaba hudu baya , shi dai yana tuki a hankali ne, mahaifiyarsa kuwa kana kallonta hankalinta a tashe yake, dan ta san me hakan yake nufi ganninsu a wannan waje a irin wannan lokacin Sunna tsayawa sojan daya ya bude masa motar ya sauko , lokaci daya suka saka gwuiwarsu daya a kasa dayar a dan dage suka dora hannayensu na hagu da dayar suka cire hulunan da suka yiwa fuskarsu katanga da gane su waye su sannan suka shiga masa sannu da zuwa hadi da gabatar da kansu daya bayan daya da kiransa da sunna *SARKI* abinda ya tsaya gani daya ne, gabatar da kan nasu da zasu yi, sunna gamawa ya bude bayan ya mikawa mahaifiyarsa hannu yana kallonta a nutse ya ce" Mah sauko" Mah ta sake zuba masa ido, a saman lebenta ta ce" Me yake faruwa ne?" Da idannuwansa ya mata alamun bai sani ba, dan haka a dole ta kamo Rauda wace take ta kale kalen kowa da mamakin toh, ikon Allah, wannan mutumen kuwa wai wanene shi? Rauda na fitowa sai ta ji tsoro ya fara kamata, saboda tana fitowa sai ta ga mutanen dake duduken nan kamar ba mutane ba? Gashi jikinsu gaba daya shigar baki ne, ga bindigogi a jikin nasu kamar wa'inda zasu je yaki? Da sauri ta dauke kanta daga bin su da kallo tana bin mama da ta rike hannunta sunna biye da ɗan maman har suka karasa kofar inda zasu shiga ya saka cod dinsa suka shiga Mama ta kaita cikin wani daki wanda Rauda ta kasa zama saman katifar dakin dan har ga Allah tsoro take ji da tunanin arzikin mutanen Da sauri Mama ta dawo inda yake ta zauna tana fadin" YUSUF me yake faruwa a cen fadar?" YUSUF dake son ya dauki hankalinta ya fice ya ce" Mama ban sani ba, an ce dai mu zo nan, Ni yanzu yinwa nake ji mama sosai fa" Mama ta sauke ajiyar zuciya ta mike tana fadin" Bari in je kicin din naku, akoy komai ko?" Kai ya gyada mata yana sakar mata murmushi yana kallonta har ta shige ciki Wayarsa ya ciro ya ajiye nan da duk wani abinda ke cikin aljihunsa sannan ya juya da sauri ya fice Yana fitowa ya samu baban mai ba gidan tsaro ya mika masa hannu Baya ya ja kadan yana kallonsa da girmamawa ya ce" Sarki ina zaka je?" Fuska ya hade sosai ya ce" Ka aike Ni ne? Bani ky!" A dole ya bashi ky din daya daga cikin baburansu sannan ya bi bayan shi da gudu, dan walahi ba zai barshi ya je cikin gari shi daya ba, zai bi shi ne har inda zai je ko su mutu tare ko su yi rai tare, shi ya yarda ana neman ran bawan Allahn nan lokaci zuwa lokaci dan tare aka harbe su da bulet , ama shi sai kasada, sam baya ji idan aka ce ya yi biyayya kuwa kamar an ce baude! Hanya suka dauka ta cikin jeji sunna keketawa da gudun gaske, bayan ya bar masu wasiyyar kar su saki su yarda a shiga a tarda mahaifiyarsa, in sha Allah zai dawo , koda shi bai dawo ba mahaifinsa zai dawo ko kuma RISLAN, domin ukun nan su kadai suke da damar shiga gidan nan bayan shi Mah na fitowa dauke da plate wanda ta soya masa kwai kafin girkinta ya kare tana fadin" Yusuf wai yanzu baka da hakurin yinwa k.........? Idannuwanta suka sauka saman kujerar da ya tashi da wayarsa da sauran abubuwasa nan zube Da karfi ta ce" YUSUF! YUSUF!" Lokaci daya tana zubar da abinda ke hannunta ta saki plate din na kwalba ya fadi kasa, Kararsa da ihun muryarta ya saka Rauda fitowa da gudu tana zarro ido ta zuba mata ido tana kallonta A lokacin Mah ta je tana ta duduba shi bata ganshi ba, hakan ya bata tabbacin lalle Yusuf ya fita sai kawai ta nemi fita a hayacinta tana ta faman son saka cod dinsa a wayarsa ama ta kasa Da sauri Rauda ta karaso tana kallonta, jiki ba karfi da kuma tashin hankalin menene wannan din kuma ta ce" Hajia, lafiya?" Mah ta kalli Rauda ta sauri dan har ta fara manta tare suke tsabar tashin hankali Da sauri ta mika mata wayar tana fadin" Dan Allah, cire min cod ki saka min numbobin nan da zan fada maki ki min kiransu, dan Allah yata" Wayar ta amsa tana kallon yannayin Mah, A hankali ya kamma hannun na Mah ta zaunar da ita saman kujera tana kallonta a sanyaye ta ce" Mama, ki yi hakuri, ki fada min numbar na bude maki, ama ki yi hakuri ko menene kin ji?" Mah dai so take kawai ta bude mata ta kira mata numbar, dan haka ta shiga fada mata cod dinsa har ta cire mata sannan ta shiga fada mata numbar Honorable Tana fara rubuta numbar sunnan ya nuna kansa da sunnan *UBANA* , ta karanta sunnan ta karra sannan ta danna kiran ta mikawa Mama ta zauna tana kallonta, dan sai ta ji anya kuwa zata iya tafiya ta barta a wannan yannayin? Wayar ba fara ringin ya daga, muryarsa wata iri a sanyaye sosai ya ce" Yusuf kun karasa wajen?" Muryarta na rawa ta ce" Aban YUSUF, Yusuf din baya nan ai, ban san ina ya je ba, gashi ya kawo mu gidan nan na jeji kuma ya fita, ya bar min wayarsa harda su katinsa na shedar dan kasa, ina ya je? Me yake faruwa a fadar dan girman Allah? Ka fada min walahi zuciyata bugawa zata yi" Rauda ta kawar da kanta dan bata so ta maida hankali kan maganar Maman, ama kuma haka kawai ta samu kanta da maimaita FADA a cikin zuciyarta "ya Salam, ya Salam, ya Salam" Honorable ya fada yana mikewa ya fice daga cikin mutane ya nufi cen bangaren matansa dan ba kowa a irin wannan lokacin , kowa yana ɓangaren Hajia tare da marar lafiyar Yana zuwa ya sake rage muryarsa sosai ya ce" Sai fa da na fada masa ,kar ya saki ya fito, Allah kadai ya san gawar fari cikin mu da sarki da shi Yusuf, ama Hajia na gannin jikin sarki ta rikice ta ce in sanar da Yusuf in yana ina ya je gidan nan ya zauna har sai Allah ya yi yadda ya yi ji sarki ya mike ko akasinsa sai ta bada umarnin Yusuf ya fito zai fito, shine ya fito?" A rikice Mah ta ce" Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, me yake damun Sarkin? Me yasa baka fada min ba Ni ai da ka san na rike Yusuf duk abinsa ba zai fita ba ko? Wayo na shiga uku yanzu yaya zan yi?" Shi dinma hankalin nasa a tashen yake ya ce" kin ga ki kwontar da hankalin ki, in sha Allah ba komai, wai sarki bashi da lafiya tun shekaran jiya yake cikin gudawa da amai matan suka rufe suka ki fada min, sai da Hajia ta matsa kan ko ina yake a kira mata shi ne amaryarsa ta zo a sace ta fada mata walahi bashi da lafiya bakina san wanda yake kansa ba, Hajia baba ta hanna a sanarwa kowa sai magani ake didika masa a boye wai ko zai tashi ya zamto sai sun wanke shi sun cenza masa tufafi dan baya jin fitar gudawar daga jikinsa, shine fa Hajia ta yi kirana ta sanar min, da na zo ban nemi kowa ba na je bangaren nasa na bude na shiga da karfi dan kiri kiri Hajia baba ta nunan yana hutawa baya so a dame shi, da na shiga na tarda shi yana cikin wani hali, dan ko gudawar yanzu ba abinda ke fita sai ruwa tsululu, karshema malamai ne kansa ana ta addu'a, na yi na yi a je asibiti kowa ya wani nuna min wai me za'a kai" Wani irin Gwauron numfashi Mah ta sauke kirjinta na dokawa Ta rasa me zata ce, Ya Salam wannan lamari na tsoratata yana kuma daga mata hankali A me aka ɗauki sarauta ne? Me suka dauki duniya ne? A sanyaye hawaye na bale mata ta ce" Ai ba Yusuf ne abin a boye ba, kai ka san in dai abinda Hajia take nufi ne kaine abin a boye ba YUSUF dina ba, su cire Yusuf a duk wani abinda suke tunani, su fida d'ana daga rikicinsu, Aban Yusuf ka san ba zai taba yarda ya zauna kai kana cen din ba ko? Dan Allah ka fito Ku zo" "Kar ki daga hankalinki, bari yanzu in fita in gani zan ganshi na dawo da shi, Ni sam bana son fitinar nan ta gidanmu, gashi dare ya yi ama kowa sai wani irin abu yake yi, kar ki daga min hankalinki dan Allah, gan.............." "Yaya, ka fa zo, Hajia na kira" AISHA TA fada sama sama sannan ta juya da sauri ta koma A dole ya katse kiran yana karra tabatarwa maman Yusuf cewar gayanan zuwa, kar ta daga hankalinta plz A lokacin da ya shigo falon Hajia, inda sarki ke kwonce, matansa na nan a dole a irin wannan lokacin, da baban malamin masallacin gidan na zaune daf da shi sosai yana maimaita kalmar shahada, hakan ya sa gabansa ya yanke ya fadi kansa ya sara da sauri ya kai dubansa wajen Hajia inda take zaune kanta a kasa da carbinta tana ja idannuwanta a rintse tana ta ambaton sunnan Allah, dan a irin wannan lokacin ko waye kai dole zaka ji tsoron wanda ya isa ya busa kuma ya janye numfashin bawa, domin kakari na fitar rai shine ya cika falon, duk irin musun da uwar gidansa ke yi bakinta ya mutu ta kafe shi da kallo ta gaza furta koda a, sauran dake zaune kuwa an umarce su su masa addu'a ko su fita dan ba'a bukatar kowa ya daga murya a wajen Sosai kirjinsa ke dokawa ya karaso da sauri ya duka ya rike hannun dan uwansa, wanda ya zamo tamkar ya dafa wani abu marar kasashi, kamar ba tsokar naman mutun ba mai dauke da kasusuwa da nama da jini, a hankali ya amshi hailalar da ake ta maimaita masa idannuwansa na kallon wajen da ya zarce tsayuwar dan Adam, sannu a hankali har yannayin dan rike hannun dan uwansa da ya yi ya saka baki daya hannunsa ya yi nauyi a hannun mahaifin Yusuf Jiki ba laka ya sake damke hannun, wasu irin hawaye suka taru a cikin idannuwansa suka shiga zubowa a hankali saman kuncinsa ya gaza dagowa kunnayensa na jiyo masa furucin malan na sanar da sako mafi dukan zuciyar mahaifiya, Mata, ya'ya, yan uwa, dangi, da jama'ar gari baki daya, cewa RAI YA YI HALINSA Kukan matan ne ya nemi hargitsa masa kwakwaluwa ya ringa jin tamkar ciwon shanyewar barin jiki zai kama shi, a birkice ya dago dubansa yana jin duhu zai mamaye shi, jiki ba karfi ya kama da kyar ya mike ama ina, abin ya zo masa kai tsaye kuma a irin lokacin da bai shirya ko tsamaci haka ba, duk da ita dama MUTUWA takenta kennan, bata zuwa a lokacin da ake tsumayinta dukda babu bawan dake zama yace zo na shirya sai wanda yake cikin halin yau i yau!, Mutuwa dai wannan mai tonon asiri a yau ta dauka, ta katse jin dadin Dubai zata nada na dubai, ta katse shan wahalar Dubai zata dora ta Dubai, mutuwa mai yanke dukan wani farin ciki ko nau'in wahala, a daidai lokacin da ya yi baya zai zube A'isha ta mike ta zuba masa ido abinda ke zuciyarta na zuciyarta, mahaifiyarta ta yi ta yi ta tashi dan ta agaji wanda take yiwa kallon shi ya rage a matsayin wanda zai hau kujerar dan uwansa ko salon kidan ya cenza domin idan har babu ɗaya tsayaye sarauta zata koma hannun kannin riga ana ji ana gani, a lokacin ne kuma Yusuf ya karaso jiki ba laka dan tun a kofa kunnayensa suke jiyo masa hargitsewar da masarautar ta dauka , a dole ya karaso yana jin gaba daya komai ya fice masa a rai, hankalinsa ya tashi, tashin hankali kala kala ya ziyarce shi, ciki harda tunanin mahaifinsa da abinda ke iya damun uban nasa Da sauri ya karasa wajen da liman ya kama mahaifinsa yana masa sannu da nasiha irin wace ake yiwa wanda ya yi rashi ya zaunar da shi daf da mamacin wanda aka rufawa zanin gado sabo dal aka kuma tsawatarwa matan dake kuka kamar zasu tada dakin da hayaniyar kukansu A hankali ya kai hwuiwoyinsa kasa, ya kama hannayen mahaifinsa ya zuba masa ido, a tausashe sosai ya ce" KA yi hakuri Abu, kar ka daga min hankali fiye da halin da nake ciki a yanzu dan Allah" dumin hannunsa dake shiga cikin nasa ya saka shi jimke hannun da karfi sosai hawayensa na ci gaba da zuba tamkar an bude pampo Hajia ta share hawaye a sanyaye bayan ta gama waya da asibiti ta dubi wajen da su YUSUF suke a tausashe ta ce" Ku ne alwalinsa, kunne ja gabarsa, Allah ya masa rahama, ku yi masa shinfida mai kyau, yanzu za'a zo a bashi kulawar da ta dace sai a kwana ana masa sauka, Allah ya jikan ka uban talakawa...." Ta karshe muryarta na rawa sosai wani hawayen na sake bale mata, da kyar ta sake sharewa tana kallon Aban Yusuf da ya karaso da taimakawar Yusuf ya duka a gabanta ya kama hannayenta, kwarai shi ya dan irin radadin da take ji, shi ya san Wacece ita, tun sunna yara sukan yi mamakin jarumcinta, ama mahaifinsu ya taba fada masu, tsarin Sarautar garinsu dole sai da jajirtaciyar mace irinta, dan kuwa a gobe gobe da safe da zarar an birne mamacin za'a naɗa wani sarkin a ci gaba da zaman amsar gaisuwa, abinda zai zamo rikici na mamaki idan har akoy masu harin kujerar, kujera kuwa tabas akoy masu harinta na wajen gida da na cikin gida A sanyaye ya ce" Ba zaki yi kuka sosai ba? Bana so abubuwa na dira maki a zuciya Hajia" Ajiyar zuciya Hajia ta sauke mai karfi tana kallonsa a sanyaye ta ce" Idan na fashe da kuka zai dawo min ne?, yaya zan yi? Aban Yusuf na rasa uwa, uba, miji, yanzu kuma yau na rasa baban d'a, tabas mutuwa tawa ce ban dandana ba, Allah ya musu rahama ya bamu kyakkyawan karshe" Yusuf dake kallon mahaifinsa a tausashe ya zuba mata ido yana kallonta Tabas bata taɓa maganar da ta shiga zuciyarsa irin ta yau ba Kansa ya dauke yana kallo likitoci suka shigo bisa jagorar A'isha, aka dora mamacin aka fice da shi bangaren da za'a kimtsa shi a cen din ne kuma za'a masa addu'a har garin Allah ya waye Sai da aka fita da shi Hajia ta riko hannun mahaifin Yusuf tana kallonsa ta ce" BELLO, ka san me yake jiranka, sai da na hanna fitowar YUSUF, ama ya fito, ka ja shi ku koma gidan nan, sai na neme ku" Wannan karon YUSUF din ne ya dubeta da kula , sannan ba da daga murya ba ya ce" Inaga ya dace ku mayar da maganar buya gefe, dan babu inda zan je ko ya je ga gawa kwonce, duk mai so ya zo ya gwada abinda ya fi iyawa, Allah ne mai komai, idan har Allah ya ƙaddara tare za'a birni gawarwakinmu a gobe buya ba zai hannamu mutuwa ba hajia " Hajia ta zuba masa ido, zuciyarta na dokawa sosai, tana hangen abinda mijinta ya fada a kan yaron da bai ga girmansa ba bai san waye shi ba, ya Allah, ya Allah A tausashe ya sake kama mahaifinsa ya mikkar ya rike shi sosai suka fita ya nufi bangarensa da shi, dan yana so ya fara samun nutsuwa kafin ya je a kwana wajen dan uwansa, Yana fitowa A'isha ta dawo da sauri ta shige ciki wajen Hajia, yaronsa kuwa da sauri ya zo ya talaba masa mahaifinsa suka kama Abu sosai suka fice da shi ba Dar ko tsoron wani ya nufo shi A'isha na shiga ta karasa wajen mahaifiyarta, a daidai lokacin Hajia ta sada kai ne hawaye sun tarun mata a cikin idannuwa sosai tana ta jan carbi tana godiya ga Allah da jarabawar da ta sameta , ta rasa yaronta Bama zata iya tashi ba bale ta je inda gawarsa take, sai dai dadin musulunci addu'a na tarda bawa a duk inda yake Da sauri ta dago jin an zauna daf da ita ta zuba idannuwanta cikin na A'isha A'isha ta dan ja numfashi tana kallonta ta ce" Hajia, waye zai fara shiga kabarin marigayi?" Da mamaki sosai Hajia ta zuba mata ido, da yannayin muryarta da ta fara raunana saboda kukan dake cin zuciyarta ta ce" Dama akoy wanda zai fara shiga sama da BELLO da YUSUF ne?" Da sauri da kuma mamaki ta zubawa mahaifiyar Tata ido, muryarta ta kasa boye mamakin ta ta ce" BELLO? Bellon da ya fada cewar baya ra'ayin sarauta Hajia?" Wannan karon hawayen dake cikin idannuwan Hajia sun samu zubowa, ta saka bayan hannunta ta share tana kallonta ta ce" Fadarsa ce, ra'ayi ne na jin dadin harshe ya fada, kuma koda baya nan inace kin san ya haihu, domin ja gabar garina kin san ko wanene ko?" A'isha ta kasa daidaita tsuguninta saboda kaffafuwanta da suke son neman fitinarta sakamakon tashin hankalin dake son damunta na amsar da ta san me ake nufi da ita wace da wahala idan har ba zata iya yin fito na fito da dangi a kan wannan ba, sai dai da kula sosai ta ce da mahaifiyar ta " dama akoy wanda ya cencata bayan RISLAN ne?, nagartar yana da ita, makaranci ne, malami ne, mai jin tsoron Allah ne, ba'a taba kama shi da wani laifi ba, kuma daidai gwargwado yana da kudi, me ake so a daurawa talakawa? Kar dai ace mashayi mazina................." Harshenta ya datse saboda zazafan marin da Hajia ta sauke mata a saman kuncinta, rai bace sosai ta ce" Asalamu alaikum, alhamdulilah mun tsaya bakin nan a free page, zamu nausa cikin labarin, domin AZAL din na gaba, rikicin na gaba, zazafar soyaya mai rikita zukata na gaba, darasi na gaba, kai ba zaka gane ba sai ka shigo mun tafi tare in sha Allah Azal 16 A sanyaye sosai Hajia ta ce" Nana, dukda sarauta ce, hakane, a lokacin da aka ɗauki kukan rasa wani ake naɗa wani, sai na ga kamar kin yi gagawa da saurin neman zurowa cikin abinda yake iya zama shafafe sannan wanda ke wanze da maza a gabanki, Wacece ke? Shin bushewar zuciyarki har ta kai wajen nan ki dubeni ki kirayi YUSUF da sunnayen nan?, kar ki saka na zama yarinya kuma wace bata tsoron a je a dawo ya zamto na zauna nima ina tada maki jiya i yau, mai kashi a jikinsa ne zai zagi wani? Ko menene shi an jima da fadin waye shi a doron kasa, tun kafin a san zai girma aka gargadi garajena a kansa, dan shi din shine tsayayen namiji tsakanin maza, ko mahaifiyarsa ba zan iya gani in kyale tana wulakanta shi ba bale ke , ki kula, ki kuma godewa Allah a zaune nake yau, da ace kaffafuwana na iya tashi a daren nan sai an nada wanda ya dace da sarautar nan kafin a yi kowace irin magana, Nana ba zan so ace a rikicin rai da rai harda jinni daya ba, na fi so ace rikicin daga wajen gida yake fitowa, ama ki zage damtse shi din cen da ya tsole maki ido muruci ne, haka kuma Allah shi ke zamani idan har da rabon RILSAN ya hau mulki zai hau a gobe goben nan ama kar ki manta a kasar nan in har d'an mace ya hau mulki sai abin ya zamo babu mazan ko daya, ki sanyayawa ranki kar ki bari a gane abinda ke zuciyarki wanda nima nake daf da ganewa a yanzu!" Gaba daya ƙafafuwan Nana nauyi suka yi mata, ta gaza motsawa daga inda take har na tsayin mintuna, sai da ta ga dare na karra yi ta mike ta fice ba tare da ta sake saka idannuwanta a cikin na mahaifiyarta ba ta nufi wajen da ta tabata RISLAN na nan ta saka aka yi mata kiransa Tunda ya karaso ya ga yannayinta hankalinsa ya fara tashi, a tausashe bayan ya bi bayanta sun karra yin nesa kadan ya budi baki ya ce" Ki yi hakuri mama, Allah ya jikan aba sarki Allah ya sa ya huta, dama mu dukkanmu lokaci muke jira, Allah ya sa bakin wahalarsa kennan, ama a gaskiya iyalinsa basu kyautawa kansu ba,mama dama yana cikin wannan halin ama suka boye?" "RISLAN, ba wannan ya kawo Ni ba, dangane da kujerar nan nake tsaye, domin kai nake so ka hau mulkin nan!" Nana ta fada kai tsaye tana katse maganar da yake yi a wani tausashe da wani karya harshe kamar mace, shi ba zai yi abu kaza kaza ba irin na maza sai da wani laluma da sanyaya magana A dan tsorace ya kalleta ya ce" Mene? Mulki? Ni kuma?" Zata bashi amsa ta yi dif sakamakon nufo hanyar da YUSUF ya yi hannunsa daya a wajen kunnansa ya aika kira , dayan hannun kuwa a dan jimke da alamu jira yake yi kawai a amsa masa kiran da ya aika Da hannunsa ya dan dagawa RISLAN wanda ya nufo shi da sauri , hakan ya sa ya dan dakata yana jira ya gama wayar Daga dayan bangaren RAUDA dake zaune idannuwa sun yi mata fulu fulu ɗan tashin hankali da tunani, ga wata bakuwar rayuwa, ko tace sabon tashin hankali na nufin nufota a tsiyace, dan Mah dake kwonce cikin wani irin yannayin da ya sakata shiga halin tsoro har ta dago kanta ta ɗora saman cinyarta a hankali tana mata karatu tana jin zafin jikin matar ya yi yawa hakan ya sa du take neman fita a hayacinta dan bata san yaya zata yi ba kuma, abin nema yake ya yiwa zuciyarta da tunanin ta yawa, sai take neman ta idasa fashewa da wani kukan da ya gama rike mata kirji da bakinta gaba daya, a irin lokacin ne wayar Mah ke ruri cikin kira'a tatausa tana neman agajin a daga Kiran farko kasa dagawa ta yi, dukda ta ga sunnan mai mahimmanci ne a jiki, sai a kira na biyu ne ta daga muryarta a cen kurya ta furta" Asalamu alaikum" Shiru ya yi da farko, a hankali ya kai dubansa fuskar RISLAN shi dinma muryarsa a tausashe sosai ya ce" Ina take?" RAUDA ta dan hadiyi abinda ke mata kai kawo a wuya, ta dubi Mah da idannuwanta ke lumshe a hankali ta ce" Gatanan" Duk irin yadda yake cikin zakuwa da son ta ba Mah wayar bai nuna a muryarsa ba, dan yanzunma Muryar wata iri da take bugun kanta ya furta" Please bani ita," A sanyaye ta cire wayar daga kunnenta ta dan dago hannun Mah da yake da dumi shima sosai ta dan matsa kasa kasa sosai ta ce" Hajia, waya ce, wannan da ya kawo mu ne, na saka maku a kunne?" Mah ta lumshe mata ido, dan kanta sarawa yake yi sosai , sannan ta dan jimke mata hannu, hakan ya tabatar mata tana nufin eh ne A nutse ta kara mata wayar tana kallon yadda Mah ke bude idannuwanta a hankali muryarta cen ciki sosai ta ce" Baka kyauta min ba" Bata san me yace ba, ta dai ga ta gyada kai, sai kuma a raunane ta furta" Allah ya jikansa, ka zo gida YUSUF" Magana ya yi mai dan tsayi, tana gyada kai kamar wani yaya da kanwarsa har dai ta saka hannunta ta dago wayar da hannun RAUDA ta kai wajen kunnen RAUDA sannan ta sauke kanta daga saman cinyar RAUDA din ta kwonta a nan dan gaba daya jikinta ya yi kamar ba nata ba ta lumshe idannuwanta tana ta addu'a a ranta Rauda dake rike da waya tana jin saukar numfashin mutun, ama gannin ba'a yi magana ba itama sai ta ki yi ta ringa sauke numfashinta a hankali Sai da ya yi niya dan kansa ya ce" Zan iya Bara maki amanar mahaifiyata kafin gobe da safe?" Idannuwanta dake lumshe ta bude da sauri tamkar wace ta yi maye ta tsaida dubanta waje daya ta kasa furta koda A ne A tausashen da yannayin yau ya haifar masa na rashin da suka yi da halin da mahaifinsa ke ciki da halin da kakarsa ke ciki ya ce" Ba zan iya fita daga inda nake a yanzu ba, ita kuma bata da lafiya, zaki iya zaunawa a gefenta ki rike wayar nan a kusa da ke, idan jikinta ya kiya ki sanar min?" Yanzun kam ji ta yi ta gaza yin shirun, a dole ta budi baki tana kallon Mah ta ce" Yaya zan yi mata?, bata da lafiya fa" Shima ya dauke numfashi a hankali ya ce" Addu'a zaki yi mata, zaki iya?" Rauda ta ja numfashi a hankali ta ce" Zan iya in sha Allah" Shiru ya yi na dan lokaci, kafin ya iya budar bakinsa kasa kasa sosai ya furta" JAZAKILAH" Kalmar da ta sa RISLAN sake zuba masa ido har ya katse kiran ya maido da hankalinsa kansa Hannu ya bashi suka yi nusabaha cikin alhinin rashin da ya zamo na su duka suka yiwa junna jaje a takaice sannan ya juya ya nufi ciki ba tare da ya karra koda kalma daya ba, sai a lokacin RISLAN ya juya ya koma wajen da mahaifiyarsa ta yi tamkar zuciyarta zata buga dan bakin ciki Yana zuwa bata tsaya wata wata ba ta saka hannunta ta make gefen keyarsa rai bace ta ce" Haka ka zabarwa kanka? Yana tsaye kana jira tamkar uban gidanka? Ka fi shi nasaba dan a jikina ba dati!, idan har haka kake so ba damuwa ka je ka bi shi kamar kare da mai gidansa, ba daraja ba mutunci, yadda yake takamar yana da jinnin sarauta a jikinsa kaima haka, kuma kai ka fi shi duk wata daraja dan baka wulakantar da kanka ba!" Kasa cewa komai RISLAN ya yi, kansa a kasa har ta gama fadan da bai san dalilinsa, fadan da baya so sam ace mahaifiyarsa ce ke yinsa, domin fada ne na rashin gaskiya, a gaban idannuwanta a dazun motocin wa'inda koda babu su baba BELLO a doron kasa kafin ya hau sai sun hau suka ringa shigowa, a irin wannan lokacin ya dace ne ace tana cen wajen Hajia an gama kimtsa wajen dan karbar bakin da tabas da yawa sun kamo hanya, ga wata rigimar da ta bilo ta rikicin sai an gurfanar da iyalan mamacin a kan rashin hankalin da suka yi na kin fadin rashin lafiyarsa, rikici dai kala kala wanda a tunaninsa a matsayinta Na mace daya a tsakaninsu zuwa yanzu tana cen tana neman mafitar da ta dace da su baki daya, sai ga wani gihitacen zance a bakinta? Allah ya yiwa wannan buri nata tsawa dan ya tabata zata jazawa kanta fitinar da ta fi karfin ta da su ƴaƴanta baki daya Gaba daya shi ya wakilci mahaifinsa , hankalinsa ya rarabu gida uku, yana yi yana lekawa wajen mahaifinsa wa'inda matansa ke zagaye da shi hankalinsu tashe baki dayansu, domin babu wace zata so ace wani abu ya same shi daga nan zuwa safe dan bakin labarima irin wannan shine ace ɗan matar da suke yiwa wani gani gani ya haye karagar mulkin nan, kai wata har ta mutu a cikinsu domin abu ne da zai iya dukan zukatansu baki daya, hakan ya sa ba su ba, ba ƴaƴansu ba, kowane rike da carbi sunna masa addu'a kuma sunna jira karin ruwan da likita ya jona masa ya kare ko ya dawo cikin hayacinsa Shi dinma wannan addu'a ita ta fi komai tsaye masa a zuciya, ba zai taba misalta halin da zai shiga ba idan muguwar Kadara ta biyo da shi ta hanyar nan, shi ya san ba zai taba yarda da wannan tatsuniyar ba, shi yasa hankalinsa gaba daya a tashe yake, sau uku yana dora hannunsa wajen kan mamacin nan a ransa yana rokon Allah, Allah ya sa ya ga alamun doguwar summa ce ya yi, haka kuma idan ya je wajen mahaifinsa ya duka daf da fuskarsa a sanyaye yakan ce" Abu, dan Allah ka rufa min asiri ka tashi, Abu rasuwar dan uwanka na san dole zata gigitaka, ama ka tashi ka ji? Ka tashi ka masa addu'a sannan ka hau mulkinka, Abu Ni din gaba dayana yaushe ka haife Ni? Dan Allah ka tashi kar zuciyata ta buga ka ji Abu?" Idan ya mike ya fito har duhu duhu yake gani, ga wasu masu tsaron da Hajia ta karro da taimakon commisionan yan sanda da sarakan da suka isa tuni an zagaye masarautar haka kuma kiri kiri idan ya motsa sukan motsa ne da shi, abin har ya fara neman zautar da dukkan tunaninsa dan ba zai iya misalta wannan tashin hankalin a kansa ba, ina ba dai shi ba Yakan kirayi RAUDA ne a dukkan motsinsa, tun tana amsa shi idannuwanta biyu, har barci ya dauketa a bayan Mah a kwonce bayan ta shinfida masu bargo sun kwonta a falon tana yi tana taba goshin Mah din da yi mata sannu har barci ya yi gaba da ita itama bai hakura ba, a cikin barcin take dagawa idannuwa a rufe ruf dan ta gaji sosai ta amsa shi sannan ta mayar da idannuwan ta rufe har aka fara kiraye kirayen sallar asubahi ta farka sakamakon farkawar da Mah ta yi suka yi ido hudu Da sauri ta shiga lalaubar hijabinta a dan birkice ta ce" Hajia kin farka? Yaya jikin?" Mah da ta jingina da jikin kujera ta sauke ajiyar zuciya tana kirkiro murmushi a tausashe ta ce" Ki daina ce min Hajia, ba zaki kirayeni da Mama ba? Ko bakya so na zama mamanki?" Kafeta Rauda ta yi da ido ta kasa cewa komai, tana kallonta ta ciciba ta tashi ta nufi ciki dan yin wanka domin ta dauri niya sunna gama sallah zasu kama hanya zata ga ubanda zai hannata fita yau a masu tsaron nan dan ba zata iya ba , zuciyarta na iya bugawa RAUDA ta dauke ajiyar zuciya ta juya zata mike wayar nan ta kuma daukan kara Sai da ta dafe goshi dan abin ya ishe ta ita kam sannan ta daga , tun kafin ya yi magana ta ce" Ta fa tashi , ta shiga wanka fa ka bar kiran hakanan mana ai da sauki ko?" YUSUF dake zaune a dakin mahaifinsa kansa na sarawa , domin su har sun fito daga masalaci, baki sun gama cika ko'ina, mutane ta ko'ina, abinda ya fi daga masa hankali magangannun dake yawo cewar shi YUSUF shine magajin garin kai tsaye , ba kwane kwane, a irin wannan lokacin da ake ciki ba'a san halin da mahaifinsa ke ciki ba kuwa ba za'a nadawa mahaifinsa sarauta ba, ba zai taba yiwuwa ba, bale uwa uba sarakai sun iso ba za'a taba dora masu tsarin da ba daidai yake da sarautar garin ba, hakan ya idasa rikita shi har ya rasa halin da yake ciki, sai gashi ana masa magana a sama sama ana fadin ya daina kiran mahaifiyarsa? Wani irin Gwauron numfashi ya sauke, bai iya cewa komai ba, duk irin abinda yake bakinsa bai iya furta wa ba, ya sake kai dubansa kan mahaifinsa wanda yake gannin tamkar da gangan ya ki amsa shi, sai dai ba maganar gangan jikin mahaifinsa ya rikice tunda suka kawo shi suka kwontar, kirjinsa bugawa yake yi gashi dama yana da ciwon zuciya dan tun a lokacin da aka so hanna shi auren mahaifiyar Yusuf aka tabatar da ciwon zuciyarsa wanda idan abu ya dake shi yake zubar da shi, sai gashi jiya wani abin ya dake shi kai tsaye wanda YUSUF yake gannin bai masa adalci ba idan har ya ki amsa shi ya mike ya amshi sarautar shi cen ya karata da ita Mikewa ya yi har kamar zai kifa ya fito falon gidan, nan ya samu matan mahaifinsa biyu, sunna ganninsa ya ga sun sada kawunansu, kuma har ya wuce basu dago ba, hakan ya sake daga masa hankali, kennan da abinda yake faruwa? Yana fitowa babbar harabar masarautar mai filin gaske wace ta fara cika da mutane masu bin nan nasa suka kuma biyo shi, a birkice ya nufi bangaren Hajia, shi ba ya dakatar da su ba, shi ba ya dakatar da mai sanar da jana'izar Sarki karfe goma na safe, da kuma nadin sarauta *MAGAJIN MAGAJI?, KAN UBANCEN BABU WANDA YA ISA YA DORA MASA WANNAN RIKICIN, INA BA ZAI YIWU BA, BA ZAI TABA YIWUWA BA!* A rikice ya shiga, ko salama bai iya yi da karfin da za'a ji shi ba sai ganninsa aka yi Da sauri tsofafi da iyaye da tarin matan dake wajen suka ringa gaishe shi da girmamawar da ta dake bata masa rai sunna barin falon har ya zama daga Hajia sai NANA a falon sannan ya kalli mai biye da shi ya mashi alamun ya koma waje Yana tafia ya karaso kan kujerar da Hajia ke zaune, cikin shigar hijab mai ruwan blue har kasa dan ya yi mata zubul da yawa har kafarta mai dauke da abin karayar a ciki ta rufe ruf hannunta rike da carbi tana ja hankalinta a kansa ya zuba mata ido a hankali ya kamo hannunta mai rike da carbin nan yana kallonta a tausashen da rabonta da ta ga ya yi mata magana a haka har ta manta ya ce" Dan Allah ki katse wannan rigimar ba zan iya ba, dan Allah ki rabani da wannan fitinar ba tafiyata bace, ki dora wanda kike so ama ba Ni ba, ku yi hakurin ya tashi , ciwon zuciyarsa ne ya tashi ba tsufa ya yi ba, ba kuma ciwon da zai hanna shi mulki bane, Hajia ba zan iya ba, bana so!" Hajia ta lumshe idannuwanta tana jin yadda zuciyarsa ke dokawa da karfi, a sanyaye ta ce" MALIK!, kana nufin Ni na isa na nada ko na sauke?, kana nufin kace a cikin wannan tsarin ka ga maganar mutun a ciki? YUSUF a jiya ko Ni ban san zan rasa d'ana ba, bale har wani d'an nawa ya fadi rashin lafiya, kana tunanin inada ta cewa a wannan tsarin? YUSUF na sha fada maka, ka sanyayawa zuciyarka ka kuma dawo da hankalinka dan babu tamtama abinda ke yawo a jikinka tabbatacce dai dai idan lokaci ya rigayi fata......" "Dan Allah ki daina min magana kamar Ni kadai na yi saura a cikin jikokin ki, kin san ko ina yaro abinda na fi gujewa kennan, ko aure ban yi ba , ban san darajar abin ba, girma ne da ya fi karfin mutun irina, Ni dan kasuwa ne, Ni mai tafiye tafiye ne, rayuwata ba irin ta sarauta bace!" Ya fada wannan karon a kasashen da ya saka Nana dubansa ta dan matso ta tausasa muryarta tana dubansa da kyau ta ce" Haka nake ta kokarin kwatantawa Hajia, ama har ta mareni, na fada mata ga RISLAN nan, ama ta kasa yarda, ko kasar nan ba zasu yarda da sarautarka ba, tunda baka boye waye kai, ka fita ka ji yanzu haka cikin rigimar da ake a kan maganar nan, Hajia, Hajia...." Ta fada tana duban Hajia ta sake fadin" Hajia kina da damar fada koda a kwonce kike a aikata maki, dan kin isa, ki bashi abinda yake so ki dora wanda ya cencenta " "Tabas a kan maganar nan, kowa zai gane Wacece Ni, na rantse maku a kan wannan sai dai raina ya fita daga gangar jikina, ku rubuta ku ajiye a yau idan girma bai kamaka ba, mahaifinka ya mike ya fansheka, kai har kana da bakin ce min ya hau sarauta? Mahaifinka ne zaka bari ya hau sarautar? Ciwonsa ba na sarauta bane, domin abu kankani na saka shi fita a hayacinsa!, idan ya hau na dan lokaci ne, kuma babu wanda ya isa ya saka Ni ce za tsarin tarihin kasata, Nana ki fita a gaban idannuwana, MALIK ka je kaima ka je kawai!" Hajia ta fada muryarta na cinkushewa kuka na neman barkewa daga bakinta hankalinta gaba daya a tashe Rai bace YUSUF ya cika hannunta ya mike har wayarsa kirar iphone ta fadi kasa ta yi ratsa ratsa ƙafarsa ya dora Mata sakamakon yada jikinsa ke wani irin abu na bacin rai, sannan ya juya har zai fito ya juyo yana kallon Nana wace ta mike din itama rai bace ya ce" Azal17 Rai bace ya ce" Ki yi gangami, ki tara majalisar dokokin kasar nan, idan mun dawo daga rakiyar Aba a yi zabe, shin zasu yarda su dora mashayi, mazinaci, kuma wanda bashi da aure saman kujerar mulkin garin nan? Ko zasu zabi naggartace malami, mai mata da ya'ya?, kar ki yarda damar nan ta kubuce maki, domin idan kika yarda suka nada min sarautar nan sai na adabi rayuwarki a kan addabar tawa rayuwar da kika yi Nana!" Yana gama fada ya yi waje ya koma bangaren mahaifinsa ya shige wanka yana ta ambaton sunnayen Allah, fiye da yadda ya saba ambata a da, dan tunda yake bai taba doguwar addu'a irin ta yau ba, burinsa yana fitowa ya ga mahaifinsa ya farka, burinsa yana fitowa ya ga komai ya zama tamkar mummunan mafarki a wajensa, dan ba zai taba iya misalta wannan mummunan labarin mai dauke da *AZAL* tiryan a kansa ba, ina shi ina sarauta? Ina shi ina sarauta jama'a? Yana fitowa daga wankan ya saka tufafi a cikin tufafin mahaifinsa, yadi ne ya dauko marar nauyi ya suturta jikinsa, kuma yadin ya dauki jikinsa sosai , rigar cema ta so yi masa kadan wajen kirji da danatsunnan hannayen, sai dai kasancewar ya san a yanzu babu wanda zai yarda ya fita a dole ya saka , a ransa yana adu'ar a gama dukkan abinda za'a yi ya je ya kai mahaifiyarsa asibiti sannan ya wankawa wannan marar kunyar marin da zai saka ta san waye shi da har zata ja masa kashedi a kan Mahaifiyarsa dan raini.....wato abubuwa sun masa yawa ne ta yadda ya kasa tantance me zai yiwa fushi, sai yake kame kame a cikin zuciyarsa kala kala Yana fitowa ya sake dukawa daf da gadon mahaifinsa ya rike hannayensa, a hankali ya dora gefen fuskarsa a tafin hannunsa na dama, yana so ya yi magana ama abin ya ci karfinsa zuciyarsa ta gaza bashi damar amayar da abinda ke ransa, sai kawai ya mike ya daidaita kwonciyar mahaifin nasa ga nufi waje yana ji zuciyarsa na sake tsintsinkewa ya nufi ayarin taron mutanen dake zaune a manya manyan shinfidu na alfarma kowa ka gani yana addu'a ne, ana zaune ga dukkan alamu shi din kawai ake jira domin a lokacin da ya karaso tun kafin ya je wajen da zai zauna manya manyan malaman garin da limamai suka mike sai sarakunan, hakan ya sa gaba daya jama'ar gari suka mike ya zamto kusan hankalin kowa a kansa da tarin idannuwa Dakatawa ya yi yana bin mutane da kallo, sai kuma ya sada kansa yana jin bayanin limamin baban masallacin masarautar da kuma masallacin idi Ajiyar zuciya ya sauke ya gyada kai ya kai dubansa wajen RISLAN da ido ya masa alamun ya karaso mana, hakan ya sa RISLAN karasowa daf da shi suka fara yin gaba dan zuwa dakin da aka killace gawar aka gama kimtsata Su ne suka fara dauka daga gaba, sai mutane hudu wasu daga tsakiya biyu daga karshe aka fitar da ita aka ajiye aka salaceta sannan aka nufi makabarta aka binne aka juyo Tunda aka wakilce shi wanda ya fara shiga kabarin mamacin yake jin tamkar hawan jinni na daf da buge shi, dan ya san me hakan yake nufi, ama kuma tarin abinda ke kai kawo a zuciyarsa a yau din ya fi komai karfi, dan duk yadda ya so hanna hawayensa zuba sai da ya zubar a lokacin da ya ga yau an turbune baba baba a karkashin kasa shikenan an kare, duk sarautar shi, duk arzikinsa, komai da komai ya tsaya a nan an kare, shikenan a yanzu mamacin sai shi sai halinsa, ko me ya aikata a duniya daga yanzu zai fara girba, ba zancen sai kiyama ya tsaya shi tasa kiyamar ta tsaya kennan, hakan ya sake rikita tunaninsa bale da ya rintse ido ya hango shi din waye sai ya ji inama zai ga mamansa a yanzu? Babu abinda zai hanna shi dukawa ya fashe mata da kuka da fadin yaya zai yi da ransa? Tamkar a mafarki suka karasa fada, kamar a mafarki yake kallon yadda aka je dakin mahaifinsa da manyan sarakuna da likitan mahaifinsa wanda ya gabatar da jiga jigan dalilan da mahaifinsa ba zai iya rike sarauta ba, wace manyan garin da sarakuna makotan garin suka yi amana da bayanin likitan da kuma abinda idannuwansu suka gane masu mahaifinsa a kwonce tamkar ba rai yana amsar ƙarin ruwa kan wani, a irin lokacin ne suka tisa keyarsa, jiri na dibansa, ya saka hannunsa da sauri ya kama kofar baban falon mahaifinsa idannuwansa a kan matan mahaifinsa su dinma a tsaitsaye suke labarin zukatansu a bayane a saman fuskar su, tashin hankalinsu da damuwarsu ya kasa boyuwa a saman fuskokinsu sunna yiwa abin kallon wani iri, sai dai basu fida rai ba, dan tunda aka sanar cewa kafin a tabatar da ko waye sarki sai an yi zaman da akan yi idan abin ya zo da rikici, sun tabata da wahala a dora YUSUF sarki a yau Cikin kamilaliyar murya bayan an yiwa dogarai dake rakadi alamun su fice sarki SHAHEED Dan Abubakar ya karaso daf da YUSUF dake tsaye ya saka kwayar idannuwansa mai dauke da abin kwali cikin nasa, dukda rawanin dake jikinsa da kuma shiga irin ta sarakai bai hanna shi sassauta rawaninsa , dudka tsaurinsa da rikon da yake yiwa rawani matsayin abin da ya fi komai kusanci da shi a suturar jiki sai da ya sassauta rufewar fuskarsa har fuskar ta bayyana a idannuwan YUSUF, fuskar da dama ba bakuwar Yusuf bace domin kyar ta san kyar ne, sukan hadu a filin basket ball a matsayin freind su buga kwalo , shi SHAHEED fuska a bayane ama babu wanda ya san waye shi sai biyu ko ukun mutanen wajen, shi kuwa YUSUF a matsayinsa da tasa darajar wace take hanna shi walawa dan ya tsani ya fita a ringa sada masan nan baya so A tausashensa da yannayin isar sa ya ce" Faduwa zaka yi ne MALIK?" YUSUF ya zuba masa ido, yana ji tamkar ya budi baki a gaban kowa yace SHAHEED bana son rainin hankali, ko ya rike shi yace ka rufa min asiri ka gudu da Ni? Ama ba dama dan kowa idannuwansa a kansa ne ciki harda Sarkin agadaz wanda ya yiwa likitan abu alamun kar ya fita dan a yau ko a sume ne sai sun tabbatar da wanda ya cencenci mulkin talakawa a kujerar da ta dace da shi, zasu ga su da wadinncen masu akidar waye asalin mai akida , sarki ko masu rike da mulki! A hankali ya kai tatausan hannunsa wajen goshinsa dake yamutsa masa ya dan murza, hakan ya sa likitan matsowa da girmamawa ya ce" Ko zaka zauna na auna jikinka sir?" Sosai ya so yin rigiza ya zube a wajen nan, koda zai dada keyarsa da kasa ne dan ya zamo ya samu summa mai kyau wace zata dan ja shi har a nada sarki RISLAN, sai kunnayensa suka jiyo masa magana ta aboki kuma tsara a wajen mahaifinsa wato Sarkin agadaz a tausashe ya ce" Ba maganar zama, in sha Allah koda a summe ne sai mun tabatar da shi a dakin taron cen, daga nan kuma sai mu tsaya da jajircewa da addu'a har Allah ya tabatar da shi a kan kujerar da take tasa, in yaso sai mu farfaɗo shi ya amshi abinda yake nasa dan aiki ne baba Malik" Hankalinsa ya dugunzuma ya tashi, ama kuma sai ya rike kansa da kyau yana binsu da kallo har aka bar shi daga shi sai SHAHEED Da murmushi SHAHEED ya mika hannunsa ya rike nasa na dama , da dayan hannun kuwa ya mayar da rawaninsa ya rufe sosai fuskarsa sannan ya masa alamun su je Bashi da yadda zai yi sai daga kafa da bin bayansa, domin ya sani dole zai je dakin cen, sai dai abinda basu sani ba shi din da kansa zai zabi RISLAN ne a matsayin ja gabar talakawan Tsatsunburum Sunna fitowa aka dora masa alkyaba fara dal mai tsayin gaske, bai ankara da sauran rigimar dake gabansa ba ya ga yamadidin mutane a kansa, duk kuwa da rasuwar da aka yi bai hanna busa ba, wato daya daga cikin abinda ya fi kona masa rai, dan ba zai taba mantawa a lokacin da aka naɗa baba baba sarauta an dawo daga binnar mahaifinsa aka saka masa busa, hakan ya sa ya fashe da kuka, yana yi tun karfinsa ama sai da aka naɗa shi, yana kuka Hajia na hawaye Honorable na taya dan uwansa kuka A lokacin da suka nufi baban dakin taro a lokacin matar Honorable mai dakin tsakiya ta yanke jiki ta fadi, sumamiya domin dif ba numfashi a tare da ita A rikice ƴaƴanta da abokiyar zamanta wace ta yi iya yinta ita din bata suman ba suka yi kanta , ƴaƴanta na kuka da kiran sunanta su hudu, yan mata uku namiji guda karaminsu , sai ya'yan uwar gidan da ita uwar gidan sunna kiran sunnanta da kokarin bata taimako, da kyar salima ta tuna da waya ta je da gudu ta dauka ta shiga kiran numbar likitar su mace wace ke duba su ta sanar mata ba lafiya a gidan sannan ta dawo ta samu itama Tata mahaifiyar kokari ne kawai take yi dan wani irin gumi ke karyo mata da tashin hankalin da ƙarara yake bayane a fuskarta, ko a jiya bata rintsa ba, a lokacin da Salimar ta tashi tana sallar dare ta ga mahaifiyar Tata zaune ta zubawa waje daya ido, da ta tambayeta sai tace mata rasuwar nan ce ta girgizata, shi yasa ta zauna sosai ta bata hakuri da sake rarashinta kafin ta je saman salayarta ta shiga gabatar da nafilfilun da suka gama zame mata jiki, dan salima babbar makaranciyar Alkur'ani ce, tana matukar ba musulunci mahimmanci, tana karatun lauya ne, wadda a yanzu take mataki na karshe, kuma mai biya mata yayanta ne, shi yasa a kulun take kokarin dan dawo da mahaifiyarta kan hanya a kan lamarin yayansu, duda mahaifiyarta bata fitowa fili ta nuna abinda yake ranta, ama ai su ko da ido ta yi magana sun san abinda yake zuciyarta shi yasa take sakata a addu'a tana nema mata sauƙin abin a wajen Allah, dan ta san ba komai ke rikitata ba sai tunanin yau ko mulki ya dawo hannunsu ba a dakinsu yake ba, dan da wahala a tsallake manya a diro kan kananun gidan, domin kuwa kannensu maza kannanu ne sosai, in dai da ran Bah karami kamar yadda suke masa kiranye, dan sunna kiran mahaifinsu Bah, sai su ce da yayansu baba Bah karfi da yaji Salimar ce ta sa sauran ma suke kiransa haka koda iyayensu basa so, ita a ganninta idan Bah karami ya samu sarauta su ne a cikin gata ba kowa ba, a yanzuma likita kawai zata zo ta duba iyayensu itama ta je dakin taro, fatanta Allah ya sa ta zamo cikin wa'inda zasu zabe shi matsayin uban talakawa, dan ba gudu ba ja da baya a san shine daidai da mulkin zamaninsu, halayyarsa wa'inda yake aikatawa na rashin dadi kuwa ita ta san in sha Allah zai daina, zai daina ne zai kuma nemi yafiyar Ubangijinsa a lokacin da lokaci bai kure masa ba, dan a kulun cikin adu'o'in wa'inda yake kyautamawa yake Azal 18 "Ka zauna aka ce mana YUSUF" shine Muryar wace ta fi kowa bashi mamaki da ya gani a wannan waje, wace ke cikin tarin taron duk wani wanda ya isa ya saka shi ko ya hanna shi, ciki harda yayunta maza da mata, wa'inda rabonsa da ya gansu da idannuwansa har ya manta, wasu lokutan sukan wucewa ta kusan junna a mota ama baya taɓa barin shi dai su gane shi, kuma rabonsa da ya saidawa masarautarsu mota tun wani taro da suka yi suka daga hankalin mahaifiyarsa ta yi kuka ya kurce su a tsarin bangon litafin rayuwarsa, sai gasu summa a tsaye kamar yadda duk wani mahaluki ke tsaye ana jira sai ya zauna kafin su zauna, zaman da aka ajiye kujera daya tak a tsakiyar filin ake jira ya zauna masu ja in ja din taron su yi, wato MAH A raunane ya sake duban Mah, a idannuwansa yana yi mata kallon kin san me suke nufi? Mah kin san ba zan iya ba, ama bakinsa ya kasa budewa bale har ya furta wannan kalamai, hasali ma shi a tunaninsa yaya aka yi ta mike ta iya fitowa? Wa ya fitar da ita? Yaya aka yi suka yarda aka fitar masa da uwa cikin zafin ranar nan? Sai kuma lokaci daya ya ba kansa amsa ta hanyar kai dubansa kan Hajia wace ke zaune cikin motar turawa ta asibiti tana kallon nasa itama Gwauron numfashi ya sauke ya shiga takawa a hankali, cike da sabon abinda ya ratsa jikinsa da karfin ikon izar da Allah ke wanzarwa a duk jinnin jinnin bale kankat ja gabar A hankali ya kai zaune saman kujerar ya lumshe idannuwansa da kansa dake sarawa kunnayensa na jin umarnin da aka bada daga Sarkin gida cewar kowa ya zauna Baban wanda ke kare yancin talakawan a rukunin mulki ta gwamnati da yawun gwamna da duk wani mai fada a ji ne ya mike ya karaso ya mika gaisuwarsa wa kowa sannan ya budi baki cike da girmamawa da jajanta baban rashin da aka yi ya dora da fadin " Sako ya same mu a jiya da dare, a lokacin har mun yi shirin zuwa wajen jana'iza da sannin wanda zai maye gurbin mamacin, sako ya same mu cewar ba shi zai hau ba yaronsa zai hau bisa tabbacin da likitoci uku suka bamu cewar eh lalle sarauta ba tashi bace dan rashin lafiyarsa ba wace zai iya jure hawa da sauka bane na cece ku ce da firgicin sarauta na yau da kullum ina fata kowa ya gamsu da bayanina kuma ya yarda da maganar ? Idan da wanda yake da ja ko tunanin akoy wani lauje cikin nadi kan wannan bayani ya yi mana bayani ta yadda zamu katse komai kafin a yi nisa da maganar" Shiru ya yi sannan ya ringa bin kowa da kallo, har kusan minti biyar, sai ya dora da fadi " Tabatuwar zancen daga gare ku zai saka Ni ajiye jayayata a filin da ya dace na ja " "An sanar mana cewa ganganci zai saka a ba wanda bai cencenci rikon mulki ba, an ce mana ana so a ba mashayi mulki? Shaye shaye fa ake nufi? Ana nufin shan giya wace Allah ya haramta shanta? Dan kuwa duk wanda ya zamo cikin maye zai iya aikata aikin da bai sani ba , an hanne mu kusantar kanmu da sha, dan sha na saka mu aikata zunubi mafi girman da zamu yi dana sani a rayuwa har mu koma ga ubangijinmu, an tabatar mana rikicin na son rai ne? An ce bayan akoy wanda ya cencenci hawa mulki ake so a ba YUSUF BELLO?, a yau muna tsaye da karfinmu dan dakatar da wannan magana, mulki zai hau wajen da ya dace ne domin rikon talaka ake magana ba rayuwar bariki ba, kamar yadda muka sani talaka rikonsa sai mai Addini, sai mai jin tsoron Allah, wanda zai kiyaye hukuncin ubangiji ta yadda zai ji kan talaka, ina da ja da wannan magana!" Yana kaiwa karshen abinda ya kawo shi ya koma kujerarsa ya zauna, a matsayinsa na wanda ya isa ya fadi abinda ya fadan shi da kansa ya fada zuciyarsa na rawa, sai dai ya zama wajibi a bi komai yadda ya dace , a ba talaka hakinsa dan ba zasu taba bari a dora wanda bai cencenci hawa mulki ba! Tunda mutumen nan ya fara magana, maganar dadi take yi masa har aka zo abinda zai kira da cin zarafi da munanawa da kuma wulakantarwa a gare shi, a irin wannan lokacin da ake zaginsa da abinda Bama shine aikin nasa ba, dan kuwa aikinsa shi dai a saninsa taba mace ne, ama baya sha, sai dai ba kowa ya san haka ba, a hankali ya maida kansa ya sada dan ba zai iya duban idannuwan mahaifiyarsa a daidai wannan yannayin ba, shin me zata ji? Yaya zata ji? Ga yan uwanta dake zaginta da abin kulun, shin yaya zata iya jurewa? Bai taba jin takaicin munanan halaya irin na yau ba, dama ta sha fada masa shi mugun aiki ana kiyaye shi, dan idan aka tashi kalubalantarka ba'a ware cewar ka yi kaza baka yi kaza ba, za'a hade jiji da jan kanwa ne a yi maka tawa tsine a duniya, gashi dai ta sake shi "Asalamu alaikum wa rahamatulah, sunana Jabiru jikan Baba sarki, kwarai nima ina ja da maganar dora mutumen da bashi da iyali wanda ake radi radin halayyarsa mararsa dadin da bai cencenci rikon daraja irin ta sarauta ba, ba zamu iya bashi sarauta ba dan bai dace ya zama sarki ba, a matsayina na dan uwan mahaifinsa wato cousint din Honorable Bello ina da ja a kan wannan magana!" Mutanen da ake yiwa kallon idan sarauta ta kubuce daga hannun famillyn Honorable hannunsu ne zata shiga kennan, wannan shine wanda idan ba YUSUF ba Honorable a wannan karni zai hau karagar mulkin da take ta jinni da jinni a kansa, hakan ya sa kowa ya fahimci ma'anar mikewarsa da kuma karshen furucinsa, ciki harda wace ta janyo dala da Gwauron dutsen wato Nana Mikewa ta yi, a matsayinta Na mace, wace take uwa daya uba daya da uban wanda ake maganar , wace duk kunnuwa suka so jin bayanin ta dan an san idan akace YUSUF an ce ita, ta yi salama da mutuntawa sannan ta fara bayani kamar haka" Kwarai dukkan abinda aka fada a kan YUSUF hakane, sannan shi din da kansa baya son mulkin dan ya san bai tashi barin aiyukan da yake aikatawa ba, duk wani wanda ya san ahalina ya san muna dauke da jarabawar da daidaiku ke cikin tsarewar ubangiji, YUSUF duk wata masifar lalacewa ta taru a kansa!" A wajen wanda bai dubeta a zabure ba daidaiku ne da suka san kwanan zancen, Hajia kuwa zuciyarta nan take ta ringa sukanta da karfi da ya sa ta rike kujerar da take sama ta rintse idannuwanta tana rokon Allah ya sa a gama taron nan kar ta lalata masu dan har jikinta rawa ya dauka Cikin wata murya da ta dauka Tata ta ce" Bayan shaye shaye har aure ya ki ya yi, kuma yana son sha'anin mata tamkar wanda zai bi daba!" Rai bace SHAHEED ya zuba mata ido, haka RISLAN Bata ki dakatawa ba ta ɗora da fadin" Da wannan nake rokon kar a bashi mulkin kasata, dan idan aka bashi bamu san yaya zata kaya ba, ga dan uwansa RISLAN, a wajen nan babu wanda bai san waye shi ba, yaro mai mutunci mai mutunta manyansa, ga addini, gashi yana da iyali, RISLAN shine ya cencenci zama sarkin kasata " Da wani shakiyin murmushi Jabiru ya mike yana kallonta ido cikin ido ya ce" To ko ke kika aika sakon nan ne?, kina nufin kanki ya yi cushewar da zaki sako mana zancen banza a nan?, kina tunanin Muna raye zaki dauki sarauta?" Irin yadda ya kare maganar yana zarro mata idannuwansa da daga mata murya sai da ta ji tamkar zata kifa a wajen, sai a yanzu wani abu ya ringa zuwa da dawowa a kanta, tana tunanin ta yi nasara ashe da sauran rina a kaba? Idan har sarauta ta fita daga hannunsu ita ta san sai ta fi kowa wulakanta a ahalin nan dan kuwa ta fi kowa tunkaho da gobara saboda sarautar nan Mai maradi kam abin ya girmami tunaninsa, takaici ya gama rike masa zuciya, hankalinsa ya yi mummunan tashi kuma ya sani ne idan har aka yi abin son rai tabas za'a samu bacin rai a wajen nan Asalin shugaban masu kare yancin talakawan ne ya mike yana son daidaita hargitsewar da wajen ke son yi, dan idan ka dauki magana ba'a katse ka sai ka isar da sakon ka, kuma idan ka kai kara ba'a bayana wa ya kai Yana kokarin dakatar da maganar Sultan SHAHEED ya mike tsaye yana bin kowa da kallo Daga yanda ya jimke sandar da ta zame masa ta sarauta zaka gane irin yadda ransa ya ɓaci A nutse ya shiga nufo filin har ya karaso tsakiya, hakan ya sa daga jibirin har Nana yin baya sosai ciki banda shugaban masu kare yancin talakawan dan dukar da kansa ɗan sarakai basu fara magana ba, kuma yana da damar rarashi idan har rai ya ɓaci, dan haka a tausashe ya ce" Allah ya taimake ka, ka yi hakuri da shige cikin maganar da aka yi, in sha Allah ba za'a kuma ba" A tausashe, sai dai kana jin furucin ka san rai a bace yake ya budi baki yana dubansa ta saman ido ya ce" yaushe muka yi zubewar da zaka tara mu, a gabanmu, ka zagi jinnin mu? Koda kuwa kana sanar da yadda aka kawo maka karra ne bamu cencenci darajantawa ba ko dan magabatanmu?" A tausashe ya yi maganar, ya yita be har karshe, yana ajiyewa Sarkin bulala da karfi ya budi baki ya maimaita yana iza maganar ya ce" A gaban sarakan kasarka zaka zagi ɗan sarki, jikan sarki? Kai din baka da kara da girmama masu riko da ayar Allah ko zaka mana tutse cikin ganganci ne?" Sarki SHAHEED ya dora da fadin" Yaya zaka ajiye mu, ka daidaita abinda bai isa rabar hanyar mu ba, dan kawai ana so a kawo darajarmu daidai da kowani dan Adam bayan Allah ne ya dora mana rawani ba wani ba?" "Kai ja baya dan talakawa ka kai uban damagarawa kurya uwar daka, ja baya dan a yi kare jini biri jini da mu ba komai bane, rayukanmu muka miko dan yaki da gaskiya babu ruwan mu da takarda, kai ja baya dai auna tsayinka da wanda ya isa kuma wanda Allah ya nada !" Sarkin bulala ya sake wage muryarsa yana fada har kamar zai fasa wajen dan kaurin murya ne da shi sosai Rai bace sarki SHAHEED ya juya wajen sarakan nan ya dukar da kansa sosai ya furta" Ku min afuwa, idan na yi laifi a hukuntani, ama idan har kuka yi shiru ina tsoron a kai ga taba darajarmu da mutuncinmu, dan idan mai turawar wawa ne mai zartarwar ba wawa bane, ana so a shigo Mu ne a boye dan a cin mana bamu gane ba? Ko rawaninmu ya yi hawan banzar da za'a sakani saukewa a bainar nasi? Innalilahi Wa ina ilaihi raj'une kalmar da take tabataciya, mudin raina har na koma gaban Ubangiji a yau ina da ja da raini da sabon salon wulakantarwa da ake son sako min dan a shigeni ta hanyar da bana so, idan kuwa sarauta karya ce na ajiye rawanina!" Yana fada ya sake sada kansa ya shiga kunce rawaninsa, kuncewar da ta girgiza duk wani wanda yake wajen ta nemi daga masu hankali bilhaki Da sauri YUSUF ya dago kansa yana gannin da gaske rawanin zai sauke? Idan har haka ta tabata an yanki yakin da har shi ba zai bari ba, a birkice ya bi ayarin wa'inda suka mike suka nufi sarki SHAHEED ciki harda shugaban masu kare yancin talakawa da sauran da suka zube kasa kawunansu a kas Yana karasawa ya damki rawanin dan sai hakuri ake badawa ama fir zai rainawa mutane hankali Da karfi ya matsi hannunsa a hankali ya ce" Kar ka soma!" Bayanan da ake yi na bada hakuri wa YUSUF Sultan SHAHEED ya dauka shima a tausashe yana kallonsa ya shiga bashi hakurin, wanda hakan ya saka Mah sakin kukanta muryarta a boye Rawaninsa ya maida masa yana dubansa, a lokacin ne Sarkin maradi ya budi baki bayan an dan sassauta rikicin ya ce" Tabas ana nufo mu da rikicin da gaba kadan mu ne zamu kai hari ba tare da an hau ko an sauko ba, ta yaya da ransa da lafiyarsa wani zai yi tunanin kai rawani wani gidan? Shin sarauta wasan yara ne? Ko an fada maku sarautarmu ta yanzu ba sai mai kokari ba? Idan nace kokari ina nufin wanda zai iya ciyar da talakawansa, dan mun jima da ɗaukan nauyin kasarmu ba tare da jiran sai an bamu ba!, waye zai rike a yanzu? Idan kunna da ja din ne har yanzu ku sai takobi ta yi aiki!" Idannuwa YUSUF ya sake rintsewa, innalilahi Wa inna ilaihi raj'une ta tabata fa, ya Salam zata tabata a kansa? Ya san za'a hau a fado ama bai yi tunanin zasu shigo da korafin ta sigar rainin da sarakai zasu ki dauka ba, Yana ji yana gani aka ringa ba junna hakuri, aka ba zaben damar da za'a yi shi da mutuntawa ba tare da an kawo harka ta rashin da'a ba, zaben da YUSUF ya koma gefe yana bin duk wanda ya dangwala masa hannu matsayin shi ya zaba da kallon baka kyauta min ba, abin mamaki harta manyan malaman garin shi suka zaba wanda hakan ya bashi mamaki ainun, har dai magana ta tabata a kansa aka kuma maidoshi tsakiyar filin nan kansa na sarawa sarakan nan suka zagaye shi da Sarkin nadi kowa ya mike nadi ya tabata a kansa, nadin da ana nadawa masu dauka na dauka a vidios, masu dauka na gidan rediyo na yin nasu aikin summa, abu dai ya zo a lokacin da bawa bai jira ko tsamata ba, duniyar YUSUF ta yi girgizar da bawa ba zai gane komai ba, har aka gama aka fice aka bar shi da mutun uku kawai, Mahaifiyarsa wace ita dinma kaffafuwanta ke neman gaza daukanta, hawayenta kuwa har sun kafe, kakarsa wace ita dinma ta sha hawayen kuma ta gaza dauke dubanta a kansa, sai SHAHEED wanda ya tsaya ne saboda abinda yake son fara sanar masa a kan ISHAK, sai dai gannin halin da iyayensa ke ciki ya gaza masa wannan furuci karshema ya yi doguwar addu'a ya rike hannunsa sosai sannan ya masa alamun zasu yi waya shima ya fice tare da taron jama'arsa suka tafi Sunna fita Hajia ta sauke ajiyar zuciya tana kallonsa, a sanyaye cike da girmama ta furta" Malik, a tsakanin sati guda zaka shirya komai na fadarka, ya dace ka yi dogon......" "Hajia......" ya fada da wata irin murya mai cike da galabaita da kuma tarin gajia da rauni Kai ta sada a hankali ta furta" Allah ya huci zuciyarka, bari na je cikin gida" Daga haka ta matsa kujerar Tata ta juya da ita ta fice da ita daga falon bayinta suka rufa mata baya da tarin jama'ar dake waje, a nan ta sake zubawa RAUDA ido, wace ke zaune tun zuwansu da Mah aka hannata shiga bisa umarnin Hajiar, sai kuma ta dauke kai suka shige ciki Kansa a kasa Mah ta saka hannunta mai dauke da dumi ta dago fuskarsa, a hankali ta sakar masa murmushi sai hawaye ya bale mata, tana kallon rigar da aka rufa masa ta alkyaba, da rawanin da aka naɗa masa da kanshin da aka fesa masa, a yau tana ganninsa da wani irin girma da daraja ne wanda bakinta ya kasa misaltawa, a raunane sosai ta ce" ...............AZAL😍😍😍😍😍 Azl 19 A raunane sosai Mah ta furta" MALIK!" Idannuwansa ya lumshe zazafan hawayen da yake ta danewa suka samu sauka a tafin hannayen nata, a hankali ya sake dora gefen fuskar nasa mai dauke da saje wanda abin rawanin ya rufe a hannun nata yana jin inama zai iya kuka wiwi irin na mata? Da ya yi ya ji sanyi a zuciyarsa A hankali ya mike ya dawo da ita saman kujerar ya zaunar da ita sannan ya duka ya dago kansa ya sake zubawa ni'imtaciyar fuskarta mai dauke da ni'imar haske irin wace d'a ke gani a duk lokacin da ya ga fuskar mahaifiyarsa ya ce" yaya aka yi kika tashi? Nace kar ki fito fa zan zo na kai ki asibiti" Murmushi ta sauke masa a hankali ta ce" Kai, yaya zaka duka , so kake a leko a dakeni ace na saka Sarki sun dukawa?"" Murmushin da bai yi niya ba ya yi, sai dai ba irin mamakeken murmushin nan bane, kadan ya yi mata ko zata ji sanyi, domin ya kula abinda take so ta gani a fuskarsa kennan, a hankali ya ce" Anya akoy wanda zai hannani dukawa a gabanki a nan duniya kuwa?......" Sai kuma ya sake dubanta ya sauke ajiyar zuciya, so yake ya tambayeta shin yaya zai yi ne yanzun? Sai kuma ya kasa, saboda ya sani ko a yanzu tana da bukatar hutawa, sannan ya san irin tashin hankalin da take ji na rashin lafiyar mahaifinsa shi yasa ya yi shiru sai ajiyar zuciya sai kuma ya dubeta ya sake jimkar hannunta A tausashe Mah ta ce" Bari in je wajen abanka, ka ga mutane zasu shigo wajenka yanzun, Please take care" Kai ya gyada mata , ta mike ta hanna shi yi mata rakiya kamar yadda ya saba a da , dan ta riga ita ta yarda dole ne yanzun cenji ya samu ta kowane fanni a rayuwar yaron nata da ita din kanta, ama duda haka tana kallo bai zauna ba sai da ta ja baban kofar ta madubi ta rufe yana tsayensa ta shiga neman y'ar amanarta A lokacin ne yan uwanta suka kuma zuwa, dan babu wanda ya tafi ashe, hakan ya bata mamaki gannin basu tafi ba, su uku rigis, maza biyu, mace guda Da wata irin mutatawar da suka jima rabonsu da yi mata irinta ko magana irin haka suka shiga yi mata barka ba tare da sun kireta da sunnan da suka lakaba mata ba tunda Kadara ta sauka a kanta da uban ƴaƴanta wato mamar soyayya Da kula sosai ƴaƴanta mai suna AGO yace" Mu karasa daga cen mu yi magana ko Andiya" A yanzunma abin kallo ta maida su, ama bata ki binsu ba dan ta sakawa ranta su je su mata wankin baban bargo ne kamar yadda suka saba Sunna zuwa da kula sosai Herde ta ce" Andiya, dangane da shirin gagarumin bikin da ya dace mu yiwa Malik da kuma nunawa duniya eh danmu yau ya kai matakin sarauta ne su yaya suka ce mu yi shawara mu ga nawa nawa ya dace mu hada sai a shiga shiri dan Bama so mu amshi ko sisin kwabo din Sarki, mune nan zamu masa matsayin iyayensa, ke a ganninki nawa nawa ya dace?" Yanzun kam da tsoron rayuwa da mamaki take binsu da kallo har sai da autansu mai bi mata ya ce" Aunty yi magana mana yanke ko nawa ne mu je mu shiga shiri dan gaskiya Ni wanda zai yi girkima sai na dauko mutun daga waje" Idannuwanta ta lumshe, ta rasa gane a wani yannayi take ciki, abinda ta sani shine yannayin da take ciki ba na farin ciki bane, dan kuwa wannan yannayi da ta jima tana mafarki a yanzu da yake bayyana kansa a gare ta a dalilin wani baban dalili na rayuwarta sai ta ji bata farin ciki da maraba da shi, a sanyaye ta ce" Biki kuma?, rasuwar da aka yi fa? Kuma kun san mahaifinsa bashi da lafiya , inaga ba wani biki da za'a yi da ya huci a masa fatan alkhairi da nauyin da ya hau kansa da addu'ar Allah yana taya shi riko" Su Dukansu sai da suka yi jim, sai kuma Herde ta ce" Hakane, an yi rasuwa, ama gaskiya koda a cen baban gida ne idan abubuwa suka lafa zamu yi taron murnar nan , dan abin a yi murna ne, Allah ya ba Honorable lafiya" A saman lebenta ta amsa, ta shiga alamun tana son tafiya Ba wani kunya Ago ya ce" Kin ga ku je cikin ku zauna mu bari mu tafi wajen mazan mu zauna , yarenma sun ce gasunnan zuwa ai da iyayensu" Yanzu kam abubuwan su sun fi karfin tunaninta, bata iya basu amsa ba sai komawar da ta yi ta shiga neman RAUDA, da kyar ta ganta zaune da wayarta a hannunta, yannayinta har yanzun bai koma normal ba dan har yanzu bata san yaya take ciki da batan uncle dinta ba, da kuma halin da kanninta yake ciki shi yasa take jira Mah ta dawo ta fada mata tana so ta je Damagaran dan ta ji halin da ake ciki da uncle dinta da kuma kanninta A nutse Mah ta yi mata salama Da sauri RAUDA ta dago, ta mike tana amsawa a hankali gannin wata mai kama da ita sosai a gefenta tana binta da kallo Kai ta sinne dan sai ta ji kallon wani iri, domin irin kallon nan ne ba karewa mutun kallo tun daga sama har kasa A tausashe Mah ta ce" Mu tafi ki karya" RAUDA tun a nan ta so fada mata tana son tafiya, ama ta kasa, ta bi bayanta bayan ta riko hannunta kamar wace ta riko wata mai yan kannanun shekaru suka nufi cen baban bangaren famillyn, sunna tafe ana yi mata gaisuwa ta mamaki, gaisuwar da a da Bata samun rabin rabinta sai idan ta shigo fadar da mijinta ko da danta, sai gashi yau ita daya dinta ana gaisheta da girmamawa ta mamaki Ajiyar zuciya ta sauke kawai ta girgiza kai, suka shige baban falon da salama a bakinsu Yaran ne kawai a falon daga mazan har matan , sun yi jigum abinsu dan babu wani mai walwala ko sakewa a cikinsu, saboda rashin lafiyar iyayensu A tare suka ringa gaishe da su Mah, saboda koda iyayensu na koyar da su wasu halayar a boye sunna da karfin gabatarwa ne a gaban idannuwansu, idan basa nan sunna jin tsoron yayarsu sosai dan bata cika shiga lamarin su ba, halayarta kusan na Bah karami ne, shi idan dai magana ta haɗaka da shi bukatarka ka kai ya gyada kai shikenan, daga nan ba kari , Amsawa Mah ta yi ita kadai da kula sosai, taba tambayar su iyayensu Yayarsu ta sanar mata sunna daki, dan haka ta dubi yayar tasu da yar fara'a a fuskarta ta ce" Salima, Please ga y'ata nan ki saka a yi mata abun kari, sannan ga ky din dakina nan ki saka a tsaftace min na san ba dai dati da kura ba " Da sauri Salimar ta amsa tana fadin" To Mah, bari in kira masu aiki yanzu a yi, bakuwa zo ki zauna a wancen falon " Mah ta yi mata alamun ta je, a dole Rauda ta nufi wani falon a zuciyarta tana mamakin fasalin ginnin da irin tsarin furniture din dake ko'ina Herde ta kasa hakuri bayan sun nufi bangaren Bah da sabon yannayin girmama Mah ta ce" baby wai wannan yarinyar fa wacece?" Mah ta kama kofar dakin da ta dan juyo da kula ta ce" Bari in ga yaya dakin yake," sai kuma ta dan saki murmushi ta ce" Lah wai Raudar ce baki sani ba? Y'ata ce fa" Daga haka ta yi shiegwarta ta bar yar uwar ta da baki bude cike da matsanancin mamaki da tunanin maganar Tata, kai ina ba gaskiya bane, bayan YUSUF ai Andiya bata kuma haihuwa ba, bata kuma haihuwa ba tabas, tunda ko yanzu ai kamar ta gabatar da wancen yarinyar ne a wajen su Salima ko? Idan yar uwarsu ce har sai an gabatar da ita anya kuwa? Jira ta yi har Mah ta fito daga dakin idannuwanta sun yi wani iri, suka shiga ta masa addu'a ta koma falo ta zauna dan yanzu ta ga wajen zama, Mah kuwa ta komawarta daki wajen Bah Tana zama da yan mintunna ya'yan yayanta da na kanninta da yarta guda da matansu suka karaso har bangaren dan haka ta mike fuska hade ta ce da ya'yan Bah kowa ya je dakinsa tunda ba komai suke yi a falon ba, ita kuma da isa suka cike falon sunna ta firarsu yan matan kuwa sai selfi din kansu suke dauka, babu mai shiga harkar yar uwarta sunna dane danen wayoyinsu, domin kar ku manta bangaren mahaifinsa babu abinda bai zuba ba, koda mahaifiyarsa ba a nan take ba bai rage su da komai ba saboda mahaifinsa da kanninsa da yake yiwa uzuri ainun, Raudah Zuciyarta na cikin hali na damuwa da kunci mai girman gaske An kawo mata abinci mai rai da lafiya da su lipton, kayan kari dai da zata iya cewa bata taɓa haɗawa kanta su ta ci ba, ama ta kasa ci sai milo ta amsa da Salima ta haɗa mata ta bata sannan ta zauna a dan nesa da ita kadan, da katon hijabinta itama , Babu hirar da suke yi, ama Salima bata tafi ta barta ba Sai da ta gama shan milo din ta sauke ajiyar zuciya ta ciro wayarta daga cikin jakar Mah a hankali ta shiga tunanin numbar da zata kira Da kyar ta tuno ta Aminu mai adaidaita, dan haka da sauri ta lalubo numbar ta danna masa kira Bata jima tana ringing ba Umar ya daga kiran yana yi mata doguwar salama A sanyaye RAUDA ta amsa, ta shiga gaishe shi kamar yadda yake gaisheta A tausashe ta ce" Aminu, yaya Abanmu an ganshi kuwa?" Aminu mai adaidaita ya ja numfashi ya ce" Walahi Hajia RAUDA har yanzu dai bamu samu labarinsa ba, ama baki ga yadda sojawa da polisawa ke kai kawo a anguwar ba, ai ki godewa Allah , Allah ya ga maraicinki ya bayyana maki mutanen nan a wannan lokacin, gashi yanzu ance wanda ya amshi abin a hannunsan nan kin ga mahaifin sarki ne, na tabata za'a ji abinda Malan Umar ke ciki bi izinillah " RAUDA ta sake sada kanta, kasa kasa take maganar sosai, ama bai hanna Salima jin abinda take fada ba, hakan ya sa ta dan kalleta sai kuma ta cire dubanta dan ba zata so ta ga kamar ta takurata ba A hankali RAUDA ta ce" Kana ji Aminu, dan Allah ka je gidan inna, ka ce da ita kar ta bari Abdul ya ji wannan abin, kuma kar a kai shi gidan nan, ka ga yanzun bana nan, idan aka kai shi na tabata Mama zata amshi shi ne ta galaza masa, ba zai iya jurewa ba, dan Allah ka min kokarin nan ka ji?" Aminu ya tabatar mata zai je da an jima ya sanarwa inna, ta yi ta godiya har sai da ya ji kansa na dagawa dan shi abin samakal alkur'an, sannan suka yi salama Tana mayar da bayanta jikin kujerar nan a hankali ta lumshe idannuwanta hadi da sauke numfashi a boye tana ji kirjinta na yi mata zafi, wani kiran ya sake shigowa A raunane ta kalli numbar Sunnan wanda ta gani ya sakata dan dagawa kadan ta daga ta kara cen ciki ta yi salama A tausashe ya ce" tare da ke wifey, kin san wani abu? Yau na zo layin baban masalaci na nan maroco na ga wata yarinya marainiya, wifey ina so mu dauketa mu raineta, dan Allah ki ce min kina so kema? Idan kin amince na dauketa na fara gyara takardun ta, a saka mata sunnanki da nawa, yarinyar shekarunta duka duka daya da wata uku, Please ce min yeah kin amince " Har ga Allah bata wani fahimtar yarensa, shiru ta yi masa har ya dasa aya, da kansa ya gane kamar bata tare da maganar da yake yi, shi kuwa ya yi kiranta da tarin zakuwa ne , dan Allah ya saka masa son y'aya, ama tun a yanzu an tabatar masa bashi da kwon baiwa wata macen bale ta haifo, shekarunsa Kusan hamsin yanzun, dan yan watanni suka rage ya cika hamsin, Allah ya jarabeshi da son RAUDA, shi Balarabe ne, ya san ba wai kyau ne ko fari ya ja shi ba, ya sani ne Allah ne ya dasa masa abin a zuciyarsa kuma yana fatan ta zamo mata a gare shi, shine damuwar ke damunsa idan ya tuna rashin haihuwa fa baban abu ne a duniyar mata, hakan na iya haɗasa masu rashin jituwa, shi din kansa ya san yana son y'aya, sai gashi yau ya ga yarinyar nan, an tabatar masa wai ana shirin mikata ne gidan marayu, dan kakarta dake rikonta ta rasu ta barta ita daya, mahaifiyarta wajen haihuwarta ta rasu, mahaifinta kuwa yana raye ama babu ruwansa da ita, jaririya ce fa, ama har ta zama kaya a hannun mutane, masu taimakon ta suke rike da ita ne suke shirin kaita yafe yana so zai je a kaita sai a mishi takardu ya zo da ita , dan ya shirya tsaf idan ya shigo Nijar auren Rauda shine abinda zai fara yi kafin komai a gabanan A tausashe sosai ya shiga magana bayan ya kashe tv din dake dan bayani da harshen larabci, ya ce" Hey, Are You crying?" RAUDA ta sake lumshe idannuwanta, a hankali hawayenta suka shiga bin gefe da gefen idannuwanta, haka kuma muryarta ta kasa fita, sai shasheka dake fita kasa kasa Gabansa ne ya fadi, da sauri ya kashe ya shiga yi mata vidio call Da kyar ta iya dagawa ta zuba masa matatun idannuwanta tana kallonsa kasa kasa A hankali ya ce" Kuka kike yi? Me ya same ki? Kina ina ne?, me ya faru? Kin san inada matsalar zuciya ko? Kar ki saka na samu attack mana , tell me" Da kyar ta bude bakinta, muryarta mai zaki da sanyi ta shiga fadin" Uncle dina, ba'a san inda yake ba, kana tune shine uwata, shine ubana, shine komai nawa........, an...an...an kawo kayansa da jini a jiki, bamu san yana raye ko ya mutu ba, ban san yaya zan yi........." Sai kawai ta fashe da kuka tana ajiye wayar ta dora kanta saman cinyoyinta tana yi sosai Ya Salam, ya Salam yake ta maimaitawa, kafin a hankali ya ce" Hey, RAUDA? Tashi ki ji" Da kyar ta dago ta dauki wayar tana kallonsa A tausashe ya ce" Ki daina kukan haka, in dai ina raye ba zaki yi kuka ba RAUDA, zan taho nan da sati Daya in sha Allah , na daina kaiwa wata biyun kin ji? Zan zo, ko a ina yake, ko nawa ake so a bada a sake shi zamu bada, mu yi ta addu'a in sha Allah, yana raye ok??????" Kai kawai take gyada masa kamar wata yarinya karama, shi kuwa sai rarashinta yake yi, har ta daina kukan sannan ya mata salama dan ba damar jan firar duba da yannayinta Gaba daya ta manta ba ita daya take falon nan ba, ita sanyin wajenma ya fara shiga kasusuwanta, a hankali ta karkata dan share hawayenta da hijabin jikinta ta ga fari kar din hannu na miko mata abin gogewa a hankali Salima ta ce" INNALAHA MA'ASABIRIN RAUDA" RAUDA ta dago jajayen idannuwanta ta sauke saman fuskar Salima, ta kasa amsar abin goge hawayen, haka kuma ta kasa daina kallonta Salima ta zauna daf da ita ta mika hannu a hankali zata share mata hawayen, RAUDA ta rintse idannuwanta, a birkice kuka ya kwace mata, a rikice ta...... 🥹🥹🥹🥹🥹🥹🥹🥹 Azl 20 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo A rikice Rauda ta mike da nufin tafia, da sauri Salima ta kamo hannunta tana mikewar itama tana kallonta ta ce" ki yi hakuri, kar ki ga ina takuraki, kuma ban tsaya dan na ji firarki ba, na tsaya ne dan bakuwar Mah kike , ita kuma tana wajen Bah, bana so na barki ke kadai kuma sai na ji wannan, RAUDA na ji sunnanki a wajen wannan da ya yi kiranki, ki yi hakuri, ki yi hakuri, ki yi hakuri, ban san girman dacin abinda kike ji ba, dan ban san dacin maraici ba, nakan kamanta a zuciyata ne, sai na ji dacin na nema ya zauta Ni, sai dai alhamdulilah kasantuwarmu musulmai Allah na saka mana hakuri da dangana komai girman rashin da zamu yi a rayuwa, ki yi hakuri, na saurari firarki kaf, in sha Allah uncle dinki ba zai rasu ba, ko a ina yake za'a samo shi, in sha Allah in dai kika samu gannin yayanmu ko? Walahi yana iya fitar maki da shi a kwana kusa, dan masu kawo rashin kirkin nan babu mai gigin kawo masa, ki yi ta addu'a, nima zan taya ki, ama ki daina kukan kin ji? Kowani tsanani yana tare da sauki Rauda, ki zauna ki ci abincin nan dan yiwa kanki horon yinwa ba zai anfaneki da komai ba sai azabtar da kanki da zaki yi, domin idan da yinwa ko ibada mutun zai yita ne wani iri, kin ji?" A tausashe sosai take maganar, kuma ta tarewa Raudar hanya, a dole sai da Rauda ta saurareta har karshe sannan ta kasa yi mata tsayaya, dan ko ba komai Salima mai kaunar ta ce, mai son ta ga ta saku ta ware ta daina damuwa ce, dan haka ta dauki nasiharta da mahimmanci sosai har ta koma ta zauna ta yi hakuri suka ci gaba da zama da Salimar, danma ita Salimar takan je jifa jifa ta ga jikin iyayensu ta dawo, sai da aka kira sallar magarib ne suka shige ciki har dakin Salimar suka daura alwallah suka shiga gabatar da Sallah Mah kam ta yi Wunin nan gaba daya tare da mijinta Ita har ga Allah ta zata kawai Herde ta yi tafiyarta ne, hakan ya sa bata wani leko ba, bata damu da nema masu abinci, bata san wainar da suke toya mata ta wuce tunanin bawa, domin kiri kiri sun kori ya'yan gidan sun baje, sunne harda su shiga kicin, ko a lokacin da amaryar Bah din ta fito dan tunda ta farfaɗo daga summar bata iya rintsawa ba, ta fito ne da nufin zuwa bangaren su Hajia baba dan ta sake yi masu sannu da zaman makokin sai ta samu taron nan na dangin Mah masha ALLAH, hakan sai ya daure mata kai sosai da sosai, ama kuma bata wani kula su ba ta wuce,dan ba zata kula wannan sabon haukan ba, abinda suka sani shine ba'a isa ba fa ace za'a kawo masu wannan matar da ta galabi zamansu da mijinsu wace a lokacin da ta zauna a tare da su ko me ta yi daidai ne a wajen miji, ko zaginta ka yi in dai ya ji sai ya saba maka, baya gannin kwaliyarsu baya yaba masu kamar yadda yake yaba mata, kai dan karshen wulakanci akoy ranar da girkinta ne ta tashi da zazabi Honorable ya shiga kicin sai da yara suka zo sunna murnar yau babansu zai yi girki suka ga haza, gashi sun tsufabma ba wani daina yin nan nan da ita ya yi ba, dan sun sani komai nata daban yake a duniyar sa yanzu kuma dan an yi nadin sarautar son kai da hauka an ba mashayi sarauta ace uwarsa zata tare masu, ba zai taba yiwuwa ba, ya mike inma yana mikewa ya amshi sarautarsa Sannan ya maida matarsa gidanta shi ya fi zame masa alkhairi.. Ratsa mutanen nan ta yi ta shige dakin Bah A lokacin Mah na saman salaya tana ta addu'a ta gama sallarta kennan, bata kai ga gama shafa adu'ar ba kunnayenta suka jiyo mata tsaki kasa kasa da fita da bugowar kofar, ita dai bata dakatar ba sai da ta gama ta mike ta je ta shafe jikin Bah da addu'a sannan ta fita ta janyo kofar dan zuwa wajen Rauda wace ta yi kiran Salima sau biyu tana tabatar mata sunna tare shi yasama bata fito ba Turus Mah ta yi cike da mamaki tana kallon sabon salo, wai kiran sallah da usur, danginta ashe sunna nan basu tafi ba? Kusan kowa kimtsawa ya shiga yi sunna mata sannu da fitowa, hakan ya sake sakata jin kamar ta dakatar da su da wannan shashancin, dan kuwa ita a memorinta babu abinda ya shige mata cikin junna, to in Bama shirme ba in maye ya manta ai uwar d'a ba zai taba yiwuwa ta manta ba! Kasa zama ta yi, a tsayen nan tana kallon Herde ta ce" Au ashe kuna nan?" Herde dukda ranta ya kiya da yar uwar Tata ta yi banza da su a falo bata nuna ba, cike da darajata kamar itace yayarta ta ce" Mu je ina kuma mu barki ke kadai Andiya?, yanzu dai mu manyan muke cewa mu tafi, su yan matan nan fa cewa suka yi ba yanzu ba, ban san me suke nufi ba" Mah ta kasa tantance Hausar Tata, yan matan ta ringa bi da kallo su uku, Musulima, Hindatu, sai Akilah, wa'inda in ba yau ba, zata iya rantsewa ko a titi suka ganta suma da wahala su shaidata dan basu wani santa ba, a lokacin da komai ya kunce tsakanin iyayensu da ita tun kafin a samu cikin YUSUF ne, to ina su ya'yan jiya jiyan nan? Bata iya cewa komai ba, yan matan kuwa da shiri suka zo kwanan suka zo, domin sun zo da tufafi, kuma wani abu da ta kula a tsakaninsu su ukun kowace bata shiga sabgar yar uwarta, ita abinda ya fi dan tsaye mata a rai to ina zata ajiye su ne?, itama bakuwa take a gidan nan fa, dakinta yana amsa sunnan nata dan baban su YUSUF yace Babu ubanda zai saka komai a ciki dan da mai dakin Da kula sosai ta ce" To, abinda dai nake gani kar su takura, kin san nan din ba gidana bane, daki daya ne da Ni sai na YUSUF, wanda na tabata ko yau a ciki zai kwana tunda ba'a gama zaman bangaren marigayi ba, " Herde ta ce" To ai ba wani abu bane dan sun zauna a dakin Mamansu, ko Musulima ta zauna, sauran su koma gida kawai dan bana so a barki ke kadai " Idannuwa kawai Mah ta lumshe dan hanna kanta shiga matsanancin yannayin da zata fito ta fadi abinda yake ranta, ta yi gumm tana binsu da kallo dan ta yiwa kanta alkawarin sai ta iya gudun ruwan kowa a cikinsu Matar yayansu ce da ta tabe baki jin maganar Herde ta ce" Aa, su zauna su duka ai ba wani damuwa bane, kin ga yanzu dole sai an tayata abubuwa kar su mata yawa, ga Honorable ga jigilar mai martaba, mu kuma da ace an bamu dama sai mu zauna mu taimaka mata, to wajen ne yanzun a nan bamu da wadatacen fili, sai an koma wajen Mai martabar in sha Allah " Magana suke yi a tsakaninsu irin na yan uwa , ama kowa neman hanyar da zai shige jikinta ne yake yi, bayan sun manta jikin nan nata sun riga sun masa dukan da komai ya ruguje dangane da su sai abinda ba za'a rasa ba wanda musulunci ya tabbatar a tsakani Bata kuma tanka masu ba har suka mike sai sake jaddada mata ta kula suke suka tafi , nan ta dawo ta cewa yan matan tana zuwa Dakin Salima ta je ta yi salama RAUDA na jin muryarta ta dago kanta da take tufkewa dan daga wanka ta fito kuma ruwa ya dan bata mata kan shine ta warware ya bushe ta shiga maida tufkewar Sassauta fuskarta ta yi sosai tana kallon Mah ta furta" Mamah, sannu" Mah ta saki nata fuskar fiye da ta RAUDA ta karaso ta zauna daf da gadon da Rauda ke zaune ta ce" Kin yi wanka ne?" RAUDA ta gyada kanta ta idasa tufke kanta ta dauki mayafin suturarta ta saka tana sake kallon Mah Mah ta ce" yaya abincin fa? Kin ci kuwa?" Ita du banbarakwai take jin tambayoyin nan idan ana mata su ana nuna an damu da itan nan, kuma har yanzu ta kasa sakewa sosai wajen amsawa, ama kuma tana amsa Mah fiye da kowa, a tausashe da girmamawa ta ce" Mun ci tare da Salima ai Mamah" Mah ta yi murmushi daidai Salima ta fito daga bayi tana gaisheta ta amsa da kula sosai ta ce" Allah ya saka da alkhairi daughter, kin kular min da yarinyata, oya tashi mu je ki kwonta dan ki huta sosai" Tana fada ta mike ne, Har Rauda ta mike itama Salima da kula ta ce" Mah, ki barta a nan mana, na ga ke kike kula da Bah, kar a barta ita kadai a dakinki, ama in ta fi son cen din to" Mah ta dubi Salima da murmushi a fuskarta, ta sake bin dakin Salimar da kallo, kwarai yana iya isar su koda su biyar ne bale su biyu kadai, ta sauke dubanta a kan RAUDA a tausashe ta ce" Zaki zauna a nan din kuwa?" Da kula sosai Rauda ta gyadawa Mah kai, Salima kuwa ta fice da carbinta ta nufi bangaren mahaifiyarta dan ta sake gannin jikinta sannan ta mata sai da safe Mah ta amshi wayarta ta saka mata numbarta ta ce" Ga numbana, idan kina da bukatar wani abu ki yi kirana ko wani time ne kin ji?" Rauda ta kuma gyada kai tana gannin abin wani iri Mah ta sake dubanta da kula sosai ta ce " dangane da neman babanki, ki kwontar da hankalinki kuma ki yi ta addu'a, in sha Allah da ba ga an samu dan sarari zan sake yiwa YUSUF maganar, na tabata zai maida hankali kin ji? Ama yanzun ki yi hakuri ki yi ta saka shi a addu'a, zan yi iya yina dan kar abin nan ya zama wani iri, kin ga babanku ya kai maganar ana ta bincike dan comissiona ya sanar min ko jiyan nan marikiyarki a wajensu ta yi rabin wuni dan shi bai yarda da ita ba, wai ko har sai da aka zane kanwar nan taki? Ni dai abinda na sani shine bi izinillah za'a same shi , sai mu yi ta saka shi a addu'a ya zamto a same sshi a cikin hayacinsa" A sanyaye RAUDA ta ce" In sha Allah Mama na gode" Mah ta yi murmushi sannan ta tafi ta barta zaune bakin gado Bayan fitar Mah ta jima sosai a yannayin nan tana ta saka da warwara, daga bisani ta gyara kwinciyarta baki bakin gadon ta yi addu'a ta shiga neman barci, dan a hankali ta ringa jin sauki a zuciyarta da samun tabbacin in sha Allah za'a ga uncle dinta , a lokacin karfe goman dare tuni ta gabato dan saura yan mintuna ta cika Salimar kuma bata dawo ba, Cen barci ya kusa daukar ta Salima ta dawo, tana jinta tana addu'a kuma tana ji ta rufa mata lalausan bargo itama ta kwonta nesa da ita ta rufan bayan ta kashe fitila, daga nan barci ya fara awom gaba da ita Sai kusan sha biyu ya nufo bangaren Bah, tare da mutanen da suka rako shi, suke tafiya tamkar ta kurame domin tunda ya shiga gabansu suka yi shiru suke tafe kowane na mamakin taku baban taku irin na rikaken sarki a tare da sarkinsu Sunna zuwa wajen get din ya dakata ya juyo a nutse da idannuwansa masu tsauri da girma da kaifi ya ringa bin su da kallo yana jin yadda suke masa salama da yare mai tafe da kirari sunna duka masa da yi masa sai da safe Ko a da idan ana masa irin haka ba baki yake budewa ba bale yau da yake ji kamar an dinke masa bakin ne? Da idannuwansa ya ringa masu alamun amsawa sannan ya juya ya nufi ciki mai gadin get din ya duka yana gaishe shi har sai da ya bacewa ganninsa sannan ya mike ya rufe get din yana murmushi a bayane ya ce" Yan garina tabas yanzu kuka hadu da daidai da ku, daga manya har yara yanzu zamu san mecece sarauta" A nutse yake ta takawa har ya karasa kofar dakin Bah Budewa ya yi ya shiga da salama ciki ciki yana kai dubansa saman doguwar kujerar da ya hangi farare tas din kafafuwa A nutse ya karasa yana jin sanyi na ratsa zuciyarsa sakamakon gannin Mah na bude idannuwanta jin tafiyar mutun da ta yi a kunnenta Dubanta ta sauke saman fuskarsa lokaci daya tana sakin murmushi a tausashe ta furta" MALIK" Idannuwansa ya lumshe yana jin sunnan da daraja a bakinta ya mika hannayensa ya tayata tashi ya zauna gefenta a nutse a hankali ya shiga ware rawanin dake kusa da habarsa sosai yana jin wata iska na ratsa shi ta ac, a tausashe ya ce" Mah, hw Are You?, yaya jikin Bah" Mah ta sauke ajiyar zuciya itama a tausashen ta mike tana fadin " Da sauki, likita yace wai zai tashi, " Tana fada ta karasa ta dauko kular abincin da ta tanadar masa ta kawo ta ajiye a baban plate mai dauke da su cokula da sauransu Yana kallonta tana zubawa har ta gama ta dago plate din tana kallonsa ya fara magana kamar haka" Zan fita da shi, in sha Allah zuwa gobe nake so da yama" Ido ta zuba masa sosai ta ce" Ka manta yanzu ba da bane?, koda za'a fita da shi sai dai Ni na fita da shi" "Mah," Ya fada yana kallon kafarta mai yi mata ciwon "Babu mai jinyarsa ne? Ina sauran suke?" Ya fada yana kallonta Mah ta yi shiru tana bashi abincin ta masa alamun ya ci, dan ko rantsuwa ta yi ba zata yi kafara ba yau bai ci komai ba Abincin ya ringa tabawa yana ta tunanin abinda ke ransa Sai da ta ga ya ajiye ta zuba masa ruwa ta mika masa ya sha ya miko mata kofin a tausashe ta ce" Ka yi hakuri da duk wani abu dake iya taba maka zuciya, zan iya jinyarsa tunda ba daukanshi ake yi cikin dare ba, ka yi hakuri bayan adu'ar bakwai sai a fitar da shi din tunda a yanzuma ba wai ciwonsa ne ya hanna shi farkawa ba, alluran da ake masa dan ya samu hutu mai nauyin gaske ne, ina adu'ar Allah ya sa kafin nan ya farka da kansa cikin nutsuwarsa, ka ji?" Kai kawai ya iya gyada mata, suka dan tattauna, gaba daya firar danarsa ne take yi, da bashi hakuri da nuna masa hukuncin ubangiji kennan, ta sake sanar masa ya bari mahaifinsa ya dawo hayacinsa ta tabata komai zai zo masa da sauki Karshe dai ita da kanta ta raka shi har dakinsa wanda Salima ce ta yi tsaye aka masifar gyara dakin har aka gama tana tsaye dan fitowar nan da ta yi ta ga jikin mahaifiyarta sai da aka yi gyaran ne ta koma shi yasa ta cika dare Da kanta ta kunna masa AC harda tunatar da shi addu'a kafin ya kwonta sannan ta tafi Tana tafiya ya samu ya tube ya shige bayi yana ta tunanin Allah ya sa kayansa dake dakin nan sa shiga jikinsa , a killace dai suke , sai dai a ajiye suke sun jima haka Tawul ya bude ya ciro cikin wrdrb din dake bayin mai madubi yar madaidaiciya Bude shi ya yi daga cikin ledarsa sannan ya nufi waje ya rataye ya shiga wanka Alwallah ya dauro ya fito ya haye salaya A yanzu YUSUF ya san ya shigo wani fage da barci bai ganshi ba, shi da kansa ya san a yanzu ya zame masa wajibi ya yi sallah ya yi addu'a ya daga hannu ya roki Ubangijinsa kariya da taimako a kan baban abinda yake wuyansa Ya jima saman salayarsa, kansa a kasa yake, ya sani a yanzu yana gaban wanda ya isa ya kifar da duniyar da yake ciki baki daya a cikin second daya, ya sani ne yana gaban wanda ya cenza masa zanen Kadara cikin yan sekwani, bai taba garajen wasa da ibada ba, dan ya yarda da kalmar LA'ILA HA ILALAH, ya kuma shaida MUHAMMADU RASULULAH SALALAHU ALAIHI WA SALAM MASOYINSA NE, ya san cewa akoy lokacin da rai zai yi halinsa domin ya yarda Kulu nafseen za'ikatul m'aut, kuma ya san akoy kwonciyar kabari bayan fitar rai, akoy ranar tsayuwa gaban Allah, kawai ya zamo cikin bayin nan wa'inda ta yiwu ba zasu samu rabauta ba? A yadda yake tunani kennan dan kuwa ka san zaka je ka fadi me ka yi? A ina ka yi? Saboda me ka yi? Kai da wa ka yi? A wajen wanda ya halicce ka, yake da ikon saka ka a wutar jahannama, ama kuma *KAKE YI DIN*.......( ASTAGFRULLAH WA ATUBU ILAIK) Yana ganawa ya je saman gadonsa ya dauki babbar wayarsa ya danna yana kallon tarin miss call din da aka jera masa Kai ya gyada yana tunanin ina shi ina iya amsa wadinnan tarin call din? Yana shirin aikawa ISHAK kira kiran SHAHEED ya shigo wayar Kwonciyarsa ya gyara ya daga kiran kasa kasa ya ce" Yaya da kiran mutun tsakiyar dare kuma ?" Murmushi SHAHEED ya yi shi dinma ya ce" kai da baka ajiye NAJEEBA da Nadia ba ai baka da time din da za'a kirayeka" YUSUF ya yi dan shiru, cikin yannayin maganarsa ya ce" Nine zaka cirewa rawani dan ka rantse sai an nadani ko?" "MALIK alkawarin Allah ne fa" SHAHEED ya fada a tausashe dan ya sani sarai YUSUF yanzun yana bukatar a tausasa masa A tausashe ya dora da fadin " kai ka san tana binka, YUSUF saboda ka guje mata ne ka kaura nesa da ita, kai ka san na san wannan ne dalilin da ya sa ka fito daga garin nan , dan ba wani rikici da ya isa ya saka ka yin nesa, ama kuma abinda ka ki yarda shine , ita fa danko ce, du inda ka yi tana biye da kai" YUSUF ya bude idannuwansa da suka yi ja saboda gajiya da tunani kala kala, kasa kasa ya ce" Kai ka san sarauta ba tawa bace, ba rayuwar da nake iya yi bace" SHAHEED ya yi murmushi ya ki bashi amsa a kan maganar nan, saima tambayar da ya masa kan awon hular dake masa YUSUF ya ce" Hula kuma? Me za'a yi?" SHAHEED ya yi murmushi ya ce" Dinkunnanka ne sun yi nisa sosai, bani da awon hularka ne ranka shi dade" YUSUF ya dafe kai, hakane fa yanzu sai ya yi dinkunnan nan ko? Da hulunan, tunda ba'a zaman fada da gajeran wando Firar dai ta dan dauki lokaci kafin su yi salama ya kwonta yana sake yin addu'a Washe gari tunda duku duku gidan ya dauki haya haya, wato bangaren Honorable Tunda gari ya fara haske kadan aka ringa shigo da takardu na neman son gannin MALIK takardun dake sauka hannun matar Honorable mahaifiyar Salima saboda a lokacin dole baki daya kowa ya fito falo baba dan a karya a kuma jirayi fitowarsa, dan sun sani ba maganar su fara neman fitina a fili bane, koda zasu yin sai dai su samu makami ba dai fito da fito da YUSUF dan BELLO ba! RAUDA na daya daga cikin wa'inda suka farka da wurin har aka yi yan aikace aikacen kayan kari da ita, a daidai lokacin sunna wajen diner baba, diner din da tabas in har zai karya a nan ne zai karya sunna ci gaba da kimtsa wajen dan Mah ta fito tuni ta kawo mata sutura ta yi wanka ta cenza , sai dai bata zumbula hijabin da Salima ta bata ba, ta dai yafa gyalen mayafin a kanta sunna dan dauki ajiye da Salima da kuma su Musulima wa'inda suka ba Salima mamaki ainun, domin a lokacin da suka shiga kicin yan matan nan uku kowace ta tambaya a bata girkin MALIK ne ta girka, hakan ya ba Salima mamaki dan a tsakaninsu a lokacin suka shiga yiwa junna kallon ke fa? WHO Are You da zaki nemi a baki girkin Malik? Me kike nufi da hakan? ................karshe dai sun zamo iyayen gida ne dan babu wace ta taɓa girkin sai bin su Salima da suke sunna kokarin saka su ko hannasu da son basu order na yadda zasu shirya komai har sai da hakan ya saka RAUDA yin murmushi ta girgiza kai dan kwarai ta gane shirmen yaran nan da abinda suke nufi, hakan sai ya bata dariya da mamakin yan matan zamani, to ita akoy wani girmemen katon da zata gyara dan ta birge? Sam mata basu san abin so bane Bama, uhum wahala!....... 🤔🤔🤔🤔🤔🤔🤔 Azl 21 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo Sunna cikin hada haɗar nan Mah ta fito dauke da kaskon turaren wutar da ta fito da shi daga ɓangaren YUSUF, Itace ta ringa gaishe da matan Bah da girmamawa da kula, su kuwa sunna amsata kadaran kadahan harda wace ta shiga jiyan ta saki tsaki ta fito falon itama, kana gannin yannayinta ka san kamar wace aka yiwa dole, ga abin karin ruwa a hannunta Mah ta ajiye kaskon dake dauke da tsumamen turaran wuta na Dolars a lungun kujeru ta zagayo ta zauna saman kujerar nan tana dan sauke numfashi, dan ta ci aiki harda na mamaki, domin tunda ta yi sallah ta kamawa YUSUF ya kimtsa mahaifinsa tas, ya dauke shi ya kai shi saman doguwar kujera suka cenzawa gadon dakin zama suka yi shinfida mai kyau, ta yi shara ta wanke bayi tas ta saka turare ko'ina suka kimtsa hatta labulaye sai da suka cenza, sannan ya maida mahaifinsa za kwontar wanda ke numfashi ama jikinsa da gumi, kuma yannayin kwonciyar da ake masa irin ta masu ciwon zuciya ne sannan ya tafi nasa dakin dan Hajia sai kira take yi tace kar ya amshi bakuncin kowa yau kuma kar ta saki ta yarda wani ya dafa masa abinci ya bashi ya ci ciki harda mutanen cikin gidan da sauransu sannan ta sanar Sarkin rawani zai zo da tufafinsa a masa rawani ita kuma zata kawo abincinsa, a haka dai suka yi salama da Hajiar Mah ta rarasheshi ya je ya yi kwonciyarsa domin a wannan lokacin da ake ta kai kawo din nan shi barcima yake yi a dakinsa, gashi har karfe tara ce zata yi Da kula sosai Mah ta ce" Ku yi hakuri jiya na kwana dakin cen ban tsaya mun daidaita ba, na yi ta jira ko wata zata shigo har barci ya daukeni, yaya kuka tsara jinyar tasa ne Hajia?" Hajia ta dago dubanta tana kallon Mah, ita abinda ya fi bata mamaki da ita kamar bata taɓa haihuwa ba caras da ita, ga shegen gayu, koda yake abin nata koda ba wanka ta dauka ba sutura na yi mata kyau ne wannan komai koshenka ba zaka kushe wannan ba Kanta ta dauke ta ce" Ai kawai ki yi jinyar , idan kuwa da Maman su Khalifa zaku raba ba damuwa dan Ni ba lafiyar gareni ba nima" Maman Khalifa ta juyo tana yiwa Hajia kallon lallema, ta dauke kai tana tabe baki dan walahi ita ba zata furta masu koda a ba a wannan shirmen, jinyarsa? A'a ita matar so ta je ta yi ama ba dai su ba! Gannin haka ya sa Mah yin dan murmushi ta mike ta nufi kicin bata kuma furta masu komai ba, ba zasu gane bane, a da ta dauki wulakanci ama banda yanzu, su da kansu sun sani banda yanzu, ba wai dan YUSUF ya hau kujerar nan ba, a'a, tun kafin ya hau ta yi watsi da wulakancin su ta fuskanci rayuwarta tunda ta gane ba zaman mutunci ake yi da ita ba ta dangana da su! Su Dukansu sun yi mamakin yadda bata basu hakurin a raba jinyar Honorable ba, sai kuma suka watsar dan sun san dama abinda take so kennan, maman Khalifa ce kawai ta kudiri a ranta ba zata bar mata mijin ba, zata hannata zaman lafiya da kai kawo tana watsa masu hannu da Bara masu kanshi kamar ita kadai ce matar BELLO ba! Mah na nufar wajen Diner ta ja ta tsaya da mamakin yan matan dake tsaye kowace ta sha kwaliya su ukun nan tamkar wa'inda suka zo gidan biki bayan gidan rasuwa suka zo Amsa gaisuwar da suke rige rigen yi mata ta yi a jimulce ta dauke dubanta ta ɗora saman RAUDA a tausashe ta ce" To nan babyn Mah" RAUDA kunya ta ji ta kamata, sai kuma wani abu da ya sakata daga kafafuwanta ta karasa daf da Mah ta nemi dukawa dan gaisar da ita, wani abu mai kama da shauki da jin wani iri kamar idan wani mai daraja a duniyar ka ya nuna maka kulawar nan A nutse Mah ta tareta ta dagota tana murmushin tsokanar da Salima ke yiwa RAUDA din, dan Salimar cewa ta yi" Iyeah, kin ga mamanki kin saku? Mah y'ar nan taki bata fira sai da ke kadai ama ko?" Mah ta sakar masu murmushi zata basu amsa kunnayensu gaba daya suka ji ana salama da rakadi na sanarwar Hajia ke tafe Har ga Allah sai da gaban Mah ya fadi, da sauri ta ware mayafin RAUDA da ta dan rankaya shi cen saman kanta ta yada mata shi sosai a saman kanta har ya rufe gashin kan nata sosai sannan ta masu alamar tana zuwa Ta kamo hanya zata tafi falon ta ja ta tsaya saboda gannin kujerar Hajia na nufowa wajen table din tana bin kowa da kallo, bayanta kuwa tamkar jela matan Bah ne kowace yannayinta na nuni da kamewa da kula dan kar su aikata wani laifin Ja ta yi ta tsaya ta shiga bin kowa da kallo, a lokacin ne Salima ta kamo hannun RAUDA suka fito sosai suka duka sunna gaishe da Hajia wace ke bin kowa da kallo ciki harda RAUDA Hajia bata amsa ba, tana kallon kowa ne daya bayan daya sannan ta budi baki ta ce" Wadinnan fa? Ban sansu ba, da wannan" Hajia mahaifiyar Salima ce ta ce" Bakin Andiya ne " "Andiya?" Hajia baba ta maimaita tana kallonta da mamaki, ba komai ya sa ta jin mamaki ba sai gannin Hajia na fadin sunnan uwar Malik haka kai tsayen nan, ba maganar kishiyarta ko abokiyar gabarta, koda da cikinta ta haife ta an zo wajen da zata dan daidaita wasu abubuwan, ita bata ce su shirya ko su yiwa mahaifiyar YUSUF biyayya ba, No, abinda take so daya ne jal, a kiyaye girman sarautar kasarta, dan a kan wannan tana iya batawa da kowa a duniyar nan! Mah ce ta budi baki a nutse ta ce" Eh bakina ne, su ukun nan ya'yan yan uwana ne, ita kuma wannan y'ata ce da nake riko" Y'ata ce da nake riko ya saka daga Hajia baba har sauran zubawa Mah ido, ciki harda Rauda wace ta sake jin wani iri a kan Mah har ta ji wani abu ya tsirga mata zuciya mai kama da rauni da jin karfi irin na soyaya na son sukar maka zuciya Abinda ke bakin Hajia ta hadiye bata yi ba a gaban mutanen, sai dai dayan bata hadiye ba, da kula sosai da kamewa ta ce" Ba damuwa, ama Wadinnan su ringa rufe jikinsu sosai, kuma su kiyaye kwaramniya idan Malik na nan, kafin a ware bangarensa daga naku!" Tana gama fada ta juyar da kujerar tana dannata ta ci gaba da fadin" A irin wannan lokacin ko me kuke yi, daga ku har yayanku ya kamata Ku bar shi, ku yi jiran fitowarsa, idan ya fito gaisar da shi kadai zaku yi dan ba lokacin ya hadu da wani abin bacin rai daga gare ku bane, in ya tafi sai ku yi kai kawon ku kafin a gama ware masa nasa bangaren?" Tana tafe a hankali ne da keken sunna biye da ita , Hajia na amsawa da in sha Allah, Mah ta yi shiru, da aunty amarya Sai da suka nufo sashensa shi da mahaifinsa Hajia baba ta yi shiru ta dakata ta masu alamun a bude mata wajen Bah Bude mata Hajia karama ta yi suka shiga ta karasa wajen da Bah ke kwonce Ido ta zuba masa zuciyarta na neman tsinkewa Da kyar ta danne abinda yake zuciyarta a kan danta ta yi masa addu'a sosai ta juyo da keken suka fito, dan ba zata tambayesu jikinsa ba domin dukkan abinda yake ciki ta sani a wajen likitansa da Mah Da suka karaso kofar dakin YUSUF dakatawa ta yi ta dubi Mah ta ce" Ki shiga ki tashe shi, dan na san yana barci, dan Allah ki masa a hankali kar ki bata masa rai, ki rarashe shi ya yarda ya yi wanka sai mu shigo da Sarkin nadi a shirya shi" Mah ta gyada kai a ranta tana ayana' Hajia da YUSUF kennan" Har zata shiga Hajia ta sake jaddada mata ta bi shi a hankali, hakan ya sake riƙe wuyan matan Bah Cen dama sun san soyayar da Hajia ke yiwa YUSUF daban ce da sauran duk wani jikanta, kuma sun sani sarai duk zafin Hajia tana shayin YUSUF , gashi yanzu ya zo wajen da duk iya shegen da ya shuka ba za'a zage shi ba ko a daga masa murya uwa uba a masa kallon banza? Ya Allah su kam haka zasu zo a banza su koma a banza kennan? Sunna ji sunna kallo yau matar da Hajia ta fi taana cikin ahali ce take yiwa magana da sanyin murya? Lalle akoy aiki ja gabansu Mah na shiga da salama ta same shi kwonce saman gadonsa ya luluba da bargo , ac kuwa ya kure sanyinsa sai barci yake yi kamar ba shi aiki ke gabansa ba Dakatawa ta yi daga nesa ta maimaita salamarta kamar sau biyu , ya yi shiru da nanauyan sauke numfashi zuwa saukakake alamun ya farka ama ya ki tashi Mah ta ce" Ai sai ka tashi malam, kai YUSUF barci ka samu yi kennan? To tashi kakarka na kofa tsaye kuma gaba dayanmu ta tiso mu ka san ba zamu zauna ba sai ta ga ka fito ko?" Idannuwa ya bude da suka masa nauyi yana tunanin me kuma tsohuwar nan ke nema da shi? Mah ta ce" Ba zaka tashi bane?" Kin motsawa ya yi, dan yannayinsa ba abin kallon mahaifiya bane, hasalima sai ya sake luluba da bargon nan sosai muryarsa da amo irin na ingarman namiji sannan a shake na mai barci ya furta" Mah, zan tashi, ina zuwa , to ama me zan mata ita wancen din?" Mah ta yi murmushi, lalle Yusuf yana neman fitina, Ta juya dan ta bashi fili ta ce" Uwar tawa ce wancen din? Zaka fada ne YUSUF, ka tashi ka yi wanka za'a shigo a kimtsaka ne, saura na ji wata gardama Allah ma kuwa in dandali bakin mutun" Shiru ya yi idannuwansa da launin ja na abin barci da guguwar da yake farkawa da ita a kulun na ALLAH Sai da ya ji Mah ta rufe kofar ya sauke ajiyar zuciya ya sauko daga gadon yana jin takaicin Hajia, dan shi itace abar su gwara ba kowa ba Wankan ya shige, wankan da ya dauki lokaci a ciki sosai domin sai da ya gama dukkan wasu uzurinsa sannan ya fito jikinsa da digo digon ruwa ya daura tawul daya a kugunsa yana rike da karami yana dan goge ruwan kansa ya karasa wajen kofar ya bude ya leka kansa ɗan ya ga a inda yai ga Mah , idannuwansa suka sauka a kan su su hudu, Hajia a saman kekenta , matan Bah a tsaitsaye babu wace ta isa ta koma ko ta zauna Dan kura masu ido ya yi, gannin du sun sada kai banda Mah da ta kawar da kanta gefe , sai Hajia wace take kallon kofar ta ce" Barka da safia Malik, na tabo Sarkin nadin ne ko ba yanzu ba?" Harara harara mai kama da jin haushi ya dan sauke mata, yana ayana' tana abu kamar wace nake da zabi salon nadan kiya ta hadani da uwata' A bayane kuwa sai ya juya ya bar kofar a bude ya komawarsa cikiya shiga saka abinda ya danganci gajeran wando da riga ta ciki da su turaruka sannan ya dauki wayarsa ya shiga amsawa ISHAK tare da bashi damar zuwa fadar da wasu takardunsa muhinmai da suturunsa tare da litafin zanensa, wanda a ciki yake zana duk wani abin da ya danganci gini Hajia ta yiwa Mah alamun ta fara shiga, sannan ta dubi sauran ta ce" Ku je falo har a gama sai na maku magana" Da wani bakin cikin hakan suka bar wajen, Hajia ta saka wayarta ta sanarwa Sarkin nadi ya karaso, sannan ta tsaya har ya shigo ya karaso dauke da wata akwati mai shegen kyau mai ruwan maroon Gaba ta yi ya bita har suka shiga falon YUSUF da salama a bakinsu su duka Sunna shigowa Sarkin nadi ya duka har kasa kansa a kasa ya shiga mikawa YUSUF gaisuwa, dan a tsaye yake da tawul baba a kugunsa da riga fara yana ta faman dannar waya yana barin sakon msg wa tarin mutanen da suke da daraja sosai a duniyarsa har suke ta rokon son ganninsa da yi masa fatan alkhairi Ido ya dan zubawa Sarkin nadi, sai kuma ya girgiza kai kawai ya dana kira ya amsawa ISHAK sannan ya katse ya juyo yana kallon Hajia wace ke masa murmushi tana kallonsa dan so take yi su yi zaman lafiya bata zo da rigima ba Kai ya dauke yana sakar mata hararar kasa kasa, hakan ya sa Mah zarro masa ido da idannuwanta ta masa alamun ya gaisar da Hajiar, hakan ya sa ya karasa yana miko mata hannu ya ce" Cava?" Murmushi Hajia ta sauke ta kama hannunsa tana kallonsa ta ce" Malik, ka ce zaka kai Ni asibiti baka kai Ni ba, kuma madarata ta kai gangara, sannan ka ga gadon nan ashe ya min tsayi sosai? Bana son sa Ni dai a min marar tsayi" duka maganar nan ta yi su lokaci guda dan burinta ta ga ya sake sakewa, ta san du rikicin da zasu yi da zarar ta yi irin haka yakan sasaubto har ya rarasheta Kafarta ya zubawa ido, a hankali ya saka hannunsa ya dan bude zannin wajen ciwon ya saka hannunsa yana kallo ya dago muryarsa cen ciki ya ce" Ciwo take maki ne?" Hajia ta dan gyada kai, hakan ya sa ya sauke ajiyar zuciya ciki ciki ya ce" To ki yi hakuri ai haka karaya take, an kusa kunceta kin ji?" A ranta dadi take ji ta yi sharar fage dan yi doguwar fira da shi, a bayane kuwa ta amsa shi sannan ta sanar masa Sarkin nadi ne gayanan ya zo dan su fara lesson na nadi sannan ya masa nadin yau ya tafi Duban Sarkin nadin ya yi ya mika masa hannu da nufin su gaisa sai ya ga ya sake dukawa yana neman fasa masa kunne da kirari Gaban goshinsa ya dafe ya je bayan kujerar ta ya shiga Turawa har kusan gadonsa sannan ya mikkar da abin kujerar ya mikar mata da kaffafuwanta ya zauna bakin Bed yana gannin yadda mamansa ke nutse , bata da sakewa sosai idan Hajia na waje, ya maido dubansa wajen Hajiar ya ce" Hala kulun sai na je na wunin nan a fada? Tun safe sai dare?" Hajia ta girgiza kai tana kallonsa ta ce" A'a, a yanzu zaka samu hutu fiye da kulun, zaka fita fada ne idan ka yi ra'ayi, ko in kana son wanzar da shara'a kai da kanka, fitarka fada ba kulun bane in ba baban abu da ya zamo dole kaine zaka tsawatarwa abin, ko karshen wata lokacin albashi dai da sauransu, kana da hutu sosai fa , shine nace wani bangaren kake so a gyara maka muhallin zamanka da iyalinka idan Allah ya nuna mana?" Bai ce mata komai yanzu kai tsaye ba, mikewa ya yi ya amshi tufafin da Mah ta fitar masa ya shige ciki Bayan ya shige din Hajia ta kalli Mah, dan a lokacin da aka bada tufafin Sarkin Nadi fita ya yi daga bakin kofar dakin ya dakata Hajia ta ce" Wannan yarinyar tun yaushe kike rikonta?, ina iyayenta suke ne?" Mah ta dubi Hajia, sai ta sada kai a tausashe ba da wani rawar murya ba ta ce" Marainiya ce, iyayenta sun rasu, ta dan kwana biyu a hannuna " Hajia ta kalleta da mamaki ta ce" Shine ba'a taba sanar min da maganar ba?, dan ban isa ba?, bayan wannan ki sani a yanzu lokaci ne da zaki tashinma kanki ki kuma san ciwon kanki, dan Ni tunda nake ban taba ganin yan uwanki sun rabeki ba, yau shine harda barin ƴaƴansu sunna yawo da wata irin shiga a falo? Ki san abinda kike ciki dan a yanzu babu wanda ba zai rabe ki ba saboda daukakar nan!" Mah ta yi murmushi bata ce komai ba, a ranta kuwa ayanawa take yi' Hajia, Ni ai ba mahaukaciya bace, kuma ina gannin zuwa yanzu idan ban biyawa wani karatun mecece duniya ba da wahala wani ya biya min, Allah dai shi kyauta kawai' Shi da kansa da ya saka wannan tufafi ya jima yana kallon madubi kafin ya dauke kansa ya sake daukan turarensa mai tsadar gaske ya bi jikinsa sosai da shi sannan ya juya ya fito da hular a hannunsa da kuma macaji dan sumar kansa bai cajeta ba da ya fito a wanka Da tatausar murya Hajia ta sanarwa mai nadin ya shigo ya bude computer hannunsa ya ringa hasko masa kalolin nadi har sai da aka tsaya kan wanda ya ji a ransa tabas ya masa ya bada damar a yi masa shi Cikin nutsuwa yake naɗa masa yana masa bayani har ya gama ya dako madubinsa ya haska masa nadin tun daga baya har gaba bayan ya gyara masa rigar da takalmin da ya saka kafa ciki da Safa Ajiyar zuciya ya sauke yana kallon Mah dake kallonsa da murmushi A sanyaye ya lumshe mata ido wanda ke nuni da zuwa yanzu kam ya fara zubar da du wani makamin yaki, dan shi da kansa da ya kalli hoton nan a madubi abinda ya karanta ba YUSUF din da bane ke zaune, wannan din wani Yusuf din ne wanda Allah ya yi wanzuwarsa a cikin jikinsa.............. Daga nan ya mike Mah ta ci gaba da masa barin turare tana masa addu'a a cen kasan zuciyarta, shi dinma yana adu'ar ne, Hajia kuwa Tata a bayane take har Mah ta gama ta dauki alkhyabarsa ta ɗora masa , ita da kanta sai da zuciyarta ta ringa tsintsinkewa, saima da Sarkin Nadi ya kai kasa kansa a kas ya shiga zuba wani irin kirari mai tayar da tsigar jiki har sai da YUSUF ya masa alamun ya bari hakanan sannan ya mike ya je ya bude kofar ya rike yana fadin" Takawarka lafiya saraki, Takawarka lafiya hamshaki, Takawarka lafiya makaranci, Takawarka lafiya uban talakawa, tafiya salama zama salama mai jinnin Bello Abubakar, talakawa na gaisheka, masu kudi na gaishe ka, sarakai sun kawo gaisuwa, kai ne mai zamani mai tafe da karfin ikon Allah, makiyan ka fadawanka suke MALIK;, ku duka ga MALIK....' Irin yadda yake jan MALIK din ya hanna da yawa dukar da kawunansu dan zumudin da kunnayensu ke masu da idannuwansu na son gannin MALIK din a yau da ya kwana ya tashi matsayin Sarki, ba nadin ba zatar da aka masa ta jiya ba, bale kannensa dake falon nan da bakin Mah , iyayensu sun dukar da kawunansu ne dan basa son ganninsa koda wasa Tsayuwa ya yi idannuwansa suka shige cikin na Salima, wace hawaye suka wanke mata fuska, jikinta har tsuma yake na shauki da farin ciki, haƙoranta a fili muryarta har kamar ba Tata ba ta furta" BAH, URS MALIK!" A hankali ya lumshe idannuwansa jin wani abu daban wanda ya zarce wanda yake ji a da a kan yan uwansa, a yanzu abinda ya ji wani mai girman da yake ji kamar ubansu yake, ko dan SALIMA ya sani a soyayar da take masa na yayanta ba karya ciki ta kire shi tashi daya da BAH ne?, a tausashe ya sakar mata murmushi bayan ya sake bude idannuwansa daga lumshewar da ya yi, sannan ya ringa daga masu hannu na gaisuwar da suke masa daga su har iyayensu Juyawa ya yi bai tsaya ya tantance waye da waye a wajen ba ya tafi tare da tarin jama'ar dake jiransa da Hajia a tsakiyarsu har ya zauna sannan ta tafi nata bangaren ta ci gaba da zaman makoki A cen kuwa bayan tafiyarsu iyayen nasu kowace shigewa ta yi giki, hakan ya sa Mah ta yi tsaye kan yan matan su zuzuba abincin kowa ya karya sannan kowa ya kama yan ayyukan gidan, har tana tsokanarsu cewar yau ba za'a kirayi mai aiki ko daya ba, masha ALLAH yan mata birjik haka, yau har Auta sai ta yi guga Da wannan suka tafi wajen abincin suka shiga zubawa, Rauda ta kasa hakuri gannin Salima ta kasa daina kuka tana kallonta ta ce" Kukan me kike yi wai?" Salima ta kalli RAUDA, dan bata yi tunanin zata wani damu da wani abinda ya shafi wani Dan murmushi ta yi ta ce" Baku ga yayanmu ba? Baki ji kamar zaki summa ba da ya fito?" RAUDA ta dan zarro ido tana kallonta, ta girgiza kai Salima za kalleta da mamaki ta ce" Wai Allah?, baki ji kirjinki na bugawa ba?" RAUDA ta sake girgiza kai harda dan dafe haba, dan ita gaskiya bata kalle shi bama bale har ta wani ji ko zata summa ko me? Gaba ta yi da plate din dake hannunta na Mah, Salima ta bita da kallo baki bude har ta bacewa ganninta, Salima ta gyada kai kasa kasa tana zuba na su Musulima ta ce" Aman a wajen nan waye bai zubar da hawaye ba fisabililahi? Kai RAUDAH"......... 😂😂😂😂🤲🏼🤲🏼🤲🏼🤲🏼🤲🏼 Azl 22 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo Cikin hukuncin ubangiji a haka cikin sama da kasa da fari da baki har aka wayi gari aka yi adu'ar sati ta mamacin, wace a tsakanin satin nan babu abinda Mah da YUSUF basu gani ba na mamaki daga mutane daban daban-daban na waje da na cikin gida , abubuwa na girmamawar da a da basu samu ba, zumuncin da a da Mah bata samu ba ta gan shi, dan har aka yi kwana bakwai din nan ras da rasuwar nan ya'yan yan uwanta na nan sunna kwana a dakinta su tashi a yi dukkan ayuka da su, kuma da zarar karfe goma ta yi a fara ba mutane damar shigowa yan uwanta tasu zo su wuni da ita sai da magariba suke juyawa, tun tana dari dari har yanzun ta saba gannin wulagawarsu ta kuma gano eh da gaske suke yi yanzu suke zumunci da ita, sunna nufin yanzu take mutun, itama sai ta ari yannayin wasan su, a ranta ta yafe masu ana zumuncin da ake son yi na nesa da nesa da dariyar hakorin,ama bata jin daga nan zasu samu yadda suke so daga gare ta, domin sunna sun harda su shawara su ringa yi tare da sauransun nan, hakan take gannin idan har ta yarda ta yaudari kanta da kanta kuma ta zama sakarya kennan! Yau tunda sassafe yan matan nan suka samu matsala sakamakon abinda daya ta dora a Tiktok saman sunnanta na Tiktok, wato Mrs mai martaba.....hakan ya sa Musulima yiwa abin dariya har ta kasa rikewa sai da ta fadi sunnan a lokacin da ta fito daga wanka daure da tawul rai bace ta ce" Iko sai Allah, wai duniya ana kani'iba in ji bahaushe, in ba cune cunen kaza ba me ya kai bakinta cikin zazafar miya?, ana gannin abubuwa a duniya masu ban mamaki, su matan mai martaba manya!" Sosai abin ya yiwa Akilah ciwo a zuciya, har ta kasa hakuri ta dubi Musulima ta ce" Da kyau tunda na iya na iya bambance abin kunya da wanda ba na kunya ba, kuma tunda lamarin nan halal ne tabatuwarsa alkhairi ne ina da yakini, sai dai kuma in wace ta fi kowa kiyaye Sannin mai kudi ne ta dawo son hada zuri'a da mai mulki dan a yanzu ta gane dan kana da kudi baka da mulki shirme ne ya sa har take iya yafe zagin da ta yi a baya na nasaba to sai ta auna shirinta tsaf mu gani, domin na fito a shirye jinnin dake yawo a jikina kuwa ba na abu ya BARNI bane sai dai na bar shi, dan ko wane ka dauka an dauko, kuma Ubangiji ya kawata halita!" Hindatu ta yi mamakin su gaba dayansu, sai a nan ta yarda da furucin mahaifiyar kan kasantuwarsu a gidan nan, tana kallon su suka yiwa junna tas ta hanyar gorace goracen abubuwan da iyayensu suka sani a tsakaninsu, sai dai basu daki junna ba, dan karrara Mah ta nuna masu gaba da suke bata so, ba zata iya dauka ba bale a kai ga dukan junna? Lalle ta yarda sunna son abinda take so, hakan ya sa ta sake zage damtse dan ita ta fi ganewa ta bi ta kasa ko zata samu biyan bukata! Haka aka yi wunin nan, yan matan kowace na falon da ta fi so tana chating dinta Salima na karatu a dakin kayan karatunsu Rauda kuwa tana zaune da wayarta ta dauko layinta wanda kowa yake da numbarta ciki harda aminiyarta Bara'atu ta saka layin tana murmushi a ranta tana ayana' ta yiwu Bara'atu sai ta min gaba, na tabata ta neme Ni, ki yi hakuri kawata, ban kashe wayata dan kar na yi zumunci da ke ba, na yi haka ne dan na baki damar fuskantar gidanki da mijinki a tsanake ta yadda ko menene zaki fi fahimtar abinki da kanki, dan na san halinki kin ga damar da ya fita ki kirayeni mu dasa fira har ki manta da girkinsa, gashi magidanci kike aure ba saurayi ba bale nace ya saba, a hakan tsaf yana iya fara jin haushinki balle idan matarsa na cika masa kullu' Har zata tura kiran numbar Bara'atu da layin, sai ta fasa ta ajiye ta shige wanka dan tana so ta je dakin Mah ta gaisheta rabonta da ita yau tunda safe da suka gaisa, ta yiwu ta sameta a dakinta ko kuma ta tafi wajen BAH? Wanka ta tsalo ta fito daure da tawul ta dauki pant baki ta saka da riga mai siraran hannaye doguwa irin mai dan lafewa a jiki din nan, rigunnan da Mah ta bata ne a cikin akwati wa'inda ake daura masu lafaya masu laushi ne, ita sai take saka su ta dora masu zumbulelen hijab, takan jita sakayau ba wani damuwa dan harda tsaga garesu wace ke hanna rigar hardeta A nutse ta dauki turarenta mai sunnan bonbon mai blue din gidan nan mai sansanyan kanshi da dadi ta shiga fesawa a jikinta tana karawa tana dan murmushi dan tana son kanshi a rayuwarta sosai sannan ta dauki hijab mai ruwan blue mai duhu sosai ta zumbula ta fitar da hannayenta ta hannayen ta saka bak'ar Safa dinta mai kwaliyar nan wace ke nuni kamar ka yi kunshi sannan ta juya hankali kwonce ta dauki wayar ta ringa gannin Msg na shigowa ta whatsup din da ta dora layin ta yi murmushi dan layinta ne da aka fi sanninta da shi, dama ta san sai ta tarda tarin msg a ciki, ta sauke layin da suke waya da Mutumen ta dan dazu yace yau zai taso daga maroko ya zo Nijar , tafiyar wuni daya da kwana ne a jirgi dan jirgin yawo ne dole ya shiga domin ya kasa samun special har gashi tana so ta sake daga hankalinta, shi kuwa abinda ya fi komai rikitashi a yanzu kennan Layin Ameenu mai adaidaita ta shiga kira tana kokarin rufe dakin da ky, sai dai yana ta ringing ba'a dagawa hakan ya sa ta nace ita kuwa a dole sai da ya daga a lokacin tana tura kofar dakin Mah da salama ta shiga ta tarda dakin a tatare fess dan har kanshin turare yake fitarwa na wuta, domin yan matan Mah basa wasa da tsafta dan babu wace take son saboda kazanta ta rasa maki A lokacin da Ameenu mai adaidaita ya daga wayar ya yi salama , Rauda ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Malan Ameenu ina ta kira shiru ko ka bar wayar a gida ka fita nema ne?" "Raudar ce ke magana?" Radau Muryar Inna ta shiga kunnuwan Rauda hakan ya sa da dan zumudi ta ce" Lah , Ameenu wajen su inna ka zagaya? Dama kiran nan da na yi maka dan nace maka ne yau zan nemi alfarma wajen Mah a kai Ni na ga Abdul sai na taboka mu tafi, ashe ka rigayeni zuwa, dan Allah bani su , ta bani shi na ji rigimamena, na tabata yana nan yana mata rikicin a kai shi aunty" Magana take yi da zumudi, ta zauna saman cafet hannayenta na dan shafa gefen fuskarta a hankali tana murmushi har ta ji salamar inna da Muryar innar wani iri, sai dai bata saka komai a ranta ba duba da yannayin girma da kuma rashin lafiya da mutun ke iya kuwa da shi, dan haka ta ce" Barka da yama Inna, ya gida yaya kwana biyu? Ina mutumen inna na kawo maki ban dawo ba ko?" Inna ta sauke ajiyar zuciya tana jin wani irin nauyi da tsoron abinda zata fada fiye da yadda ta sanarwa uwarsa kai tsaye ba wani kwane kwane, sai take jin kamar Rauda zata fi koya shiga tashin hankali idan ta ji abin nan, sai dai ba yadda zata yi dole zata sanar mata da fatan Allah ya sa hakan zai zamo sanadiyar maganin damuwar A tausashe sosai inna ta ce" bari, bari y'ar nan wahali kin ganshi ya zo Malan Ameenu ya sameni bana nan, dan yanzun nan daga gidan mai anguwa na sake fitowa, yau din nan ruwa bai shiga cikina ba bale abinci, na rasa ta inda zan dafa matsalar ban bale har na ga mafitarta, na bayar a min rokon Allah nima ina ta yi, mijin rabona da shi tun jiya da na kai shi makaranta na dawo daukansa malan yace ai ya jima da fita shi ya zatama Ni din ce na je daukansa, y'ar nan na yi kuka na yi kuka na yi cigiya ban ganshi ba, yan anguwa sunna ta tayani dan ko yanzu da Ameenu ya zo mun leka Ni da innar baraka ne gidan mai anguwa dan tun jiyan muka je muka kai cigiya harda gidajen rediyo ama shiru kake ji ba'a da labarinsa ba'a ganshi ba" A hankali RAUDA ta dakatar da murza gaban goshinta da take yi, muryarta na gaza fita, da kyar da dan karfi daidai lokacin da Mah suka nufo dakinta ita da MALIK, sanye cikin shigarsa ta sarauta, dan shigowarsa kennan saboda likitan da aka kawo daga kasar waje sun zo da likitoci biyu shine suke son takardun Bah da aka masa bincike na lafiyarsa kaf, takardun kuwa a wajen Mah suke a cikin akwatinta ta dakinta dan tunda ta zo idan aka bata ko menene basa takan zo nan ta adana gudun kar a batar a dakin nasa dukda ba kowa ke shiga ba sai ya su ya su, shine ta mike dan ta zo ta dauko ama yannayinta sai a hankali, domin karfin Hali ne Mah ke yi fiye da kowa a gidan nan, dan bata so ko kadan ta nunawa YUSUF bata da lafiya ko wani abin dan ta tabata idan ya ga haka zai tare a kanta ne, bayan yanzu da da ba daya bane, shine fa da ta mike ya kula kamar tana layi ya mike bai yiwa kowa magana ba yake biye da ita ita din da kanta sai da ta ganshi ta yi masa murmushi, shima ya mayar mata ama ta ga alamun ba zai koma ba sai kawai ta yi hakuri suka jero suka nufo dakin nata dan ba wani nisa tsakanin dakinta da bangaren Bah, sunna kawowa daf da kofar zata bude ne ta ji maganar RAUDA sama sama hadi da ruwan murya mai nuni da kuka Raudar na fadin " Inna, wai Abdul din ne ba'a gani ba tun jiya? Tun jiya bai kwana a gida ba ama ba'a sanar min ba? Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une ganinan zuwa Inna ganinan " Tana fada ta mike daga zaunen da take ta shiga neme nemen abinda bata ajiye ba, sai da ta tuna jakarta karama na dakin Salima da sauri ta nufi hanyar fita tana tunanin tabas ba zata rasa kudi a jakar ba Tun kafin ta bude kofar Mah ta bude ta shigo dakin hakan ya sa RAUDA ja baya da sauri dan bata tsamaci gannin mutun ba, sai kuma YUSUF ya shigo shima kamar yadda Mah ke kallon RAUDA haka shima ya dubeta ya dauke dubansa yana ɗorawa saman fuskar Mah wace ta fara magana tana kallon RAUDA da fuskarta ta cika da hawaye a tausashe sosai ta ce" Lafiya na ji kamar kina kuka ga kuma fuskarki da hawaye?" A hankali Rauda ta kifta idannuwanta, hawayen suka sake zubowa, ta kasa rike abinta sai kawai ta karaso ta rike hannun Mah dan ta sabar mata da haka tana kallonta ta ce" Mah, Abdul ne , Abdul ne ba'a gani ba wai tun jiya kin san wajen kakarsa na kai shi, to ban san ba'a ganshi ba tun jiya, shine take fada min yanzu da na kira, dan Allah Mah ki yi hakuri yau na fita na je na neme shi, sannan ki bani dama na sake bincikar uncle dina, zan dawo Mah ama zan nemo su, dan Allah ki barni na je dan su din duniyata ne, Abdul bashi da cikakkiyar lafiya kar aje ...kar aje ya fada wani waje ya rasu........." sai kawai ta barke da kuka ta yi cikin Mah ta rukunkumeta..... Ita dai idannuwanta a rintse ta ji kamar zasu fadi kuma sai ta ji su basu fadin ba , tana dai jin Mah na dadaba bayanta tana mata shiiiiiitttt kamar wata baby bayan a halin nan da take ciki bata jin shiiiiiiiii zai saka ta yi shiru, sai kawai ta idasa rikicewa tana kuka bilhaki tana kiran ta shiga uku Har sai da abin ya ishe shi sosai ya girgiza kai a riken da yake da su ya dan yi gyaran murya da kakaurar muryarsa ya ce" Dan dagata mana ke kar ki kayar da ita" Dif ta yi da kukan da take rairawa wai ita ta ji dadin rungumar uwa, har sai rusheshiyar Muryar nan ta wani katse ta, dan haka ta dan dakata sannan ta dago a hankali tana za sauke ajiyar zuciya, nan ta ga daga ita har Mah din a saman kaffafuwansa masu ɗauke da takalmin fata da damatsunnan hannayensa dake sanye cikin lalausan yadi blue an yi gari da yar ciki ɗinkin sarakai, sai rawaninsa da har ya shafi kanta suke, daga ita har Mah din, karfin rungumar da ta kai ta damki damtsunna ashe nasa ne, hakan ya sa da sauri ta saki ta yi baya tana jin faduwar gaba da dokawar zuciyar da Salima ke yawan fadi a kan yayan nasu Mah ta dan daki gefen hannunsa ta ce" YUSUF kar ka tsoratar min da yarinya mana, zo nan yar gidan Mah taho babyna" Mah ta fada tana karasawa wajen kujerar dakin ta zauna Shi abin ya ba mamaki, wai Babyna, ita sam bata wani ji mamaki ba domin ba yau Mah ta fara kiranta da sunnan ba, dan haka ta karasa ta zauna daf da Mah din ta sada kanta Mah ta kama hannayenta tana kallonta da kula ta ce" Bana son yawan kukan nan RAUDA, saboda mace kike kalubalan rayuwa Allah na iya zubo maki masu girman gaske kin ji? Tabas na san akoy tashin hankali, ama zan fi so ko menene ki fara dubansa da jajircewa, dan kuka da saka damuwa a rai na saka mutun ya kamu da ciwo marar magani dan ciwon stressa ya fi komai kashe bawa , maganinsa kuwa shine baban abinda yake mystere kin ji?" A hankali RAUDA ke gyada kanta Mah ta ce" Zaki iya yin hakuri a jima a yi magariba mu je tare ko a saka direba ya kai ki sai na tardo ki?" A tausashe ta ce" Mah, ina so na je sai na fara dubawa kafin ki karaso" Mah ta yi murmushi ta ce" To ina da ina zaki duba din?" RAUDA ta gyara zamanta ta ce" Zan duba makarantar su, mu yi maganar da malamin su, sai kuma mu duba ko'ina a anguwannin na tsakanin gidan da makarantar tasu" Mah ta gyada kai ta ce" To shikenan, tashi ki bude cen akoy abayoyi ki saka abaya a cikin hijabin nan kar ki fita daga ke sai rigar nan a kasa dan ana ganewa rigar bata da nauyi, bari na yiwa direba magana sai ya ga inda ya ajiye ki in an jima ya zo ya daukeni mu nemo Abdul dinmu ko?" RAUDA ta mike ta ja hijabinta ta yi masa diban albarka a gaban mutane , a gaban mutane jama'a dan sam.ta sha'afa a dakin nan ba daga ita sai gyatumarta bane, da maza a tsaye kikam jama'a ta je wajen akwatin ta bude ta shiga dubawa har ta ciro bayar da aka ce ta dauko ta juyo ne ta ga kato a dakin nasu wanda sam ta manta yana wajen, Mah na bashi takardu tana masa bayani hankalinsa a kan Mah din Da sauri ta juya ta diba ta yi bayi da dan gudu har kamar zata kifa, hakan ya sa Mah dagowa ta rakata da kallo, shi kuwa ya yi tsai har sai da ta mako kofar bayin gam ya rintse idonsa sannan ya bude ya gama amsar sakon Mah yana kallonta a tausashe ya ce"Mah ina zaki je?" Mah ta idasa bashi takardun ta ce" Binta zan yi YUSUF ka ga maganar uncle din nan nata tunda abanka ya kaiwa comitionna bamu ji komai ba, gashi yau fa kwana tara cif , ga wannan tashin hankalin kuma , bana so wannan abin ya taba lafiyar marainiyar Allah, ina mata fada ne dan na karfafi gwuiwarta, ama a gaskiya tana da kokari dan ba kowa zai iya jurewa haka ba," A tausashensa, ya sake budar bakinsa yana magana ta fito daga bayin ta je dan ta saka hijab dinta, ya ce" Ki tura min numbar wanda aka kirayan, zan shiga maganar, sannan ta zauna zan saka a dubo mata *d'anta*! Domin babu inda uwata zata je ba tare da Ni ba." Yana fada ya juya yana tafiya ne, maganar da yake tunanin a kasa kasa yake yi ta cika dakin ne, hakan na nufin RAUDA ta ji abinda ya fada daya bayan daya a tare suka bi shi da kallo, kafin Mah ta juyo inda take tsaye ido na mata ruwa ta karaso tana dubanta ta ce" Hi people Azl 23 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo Mah na dubanta murya a tausashe da yannayin son rarashinta ta ce" My daughter, zaki iya hakuri mu ga abinda zai yi? Idan bai yi wani yunkuri ba na maki alkawarin raka ki da lokacina da komai da ya dace dan mu nemo su,zaki iya hakura kuwa mu ga abinda zai yi?" Nauyin Mah ya rufe mata zuciya, duk irin abinda take ji a zuciyarta sai ta ji ta gaza yi mata musu, ko ba komai masoyi ai ba makiyi bane , sai dai wani irin abu da ya tokare nata zuciya na haushin YUSUF mai karfi ne, ta rasa me zata yi tunani a kansa bayan ta tabatarwa Mah zata yi jira Mah din ta shige wanka sai ta fice ta tafi dakin Salima dan ta fi jin nutsuwa a cen, bata san me yasa jininsu bai hadu ba da yan matan gidan nan, Yaren kuwa tsakaninta da su idan sun hadu su gaisheta ta amsa dan bata cika shiga sabgarsu ba, bale abinda ta kula in dai sun fito tare Salima ta ga mahaifiyarta takan daina yi mata magana har su bar wajen, bata san me ya sa ba, abu daya ta sani shine irin yadda ta rayu da Mama ta dauki darusa da yawa na zaman duniya, kuma bata tunanin akoy wani abu da zai iya tunkaro ta ya shige mata duhu Tana komawa ta dauko Alkur'anin Salima ta zauna ta shiga karatu, tun tana yi a fili har ta koma a zuciyarta, a hankali ta ringa jin salama da sansanyan tunani a kan damuwarta, ita fa a yanzu ba zata ce damuwar rashin wani a kusa ta fi damunta ba, ta fi kyautata zaton damuwar rashin Sannin halin da mutanen da suke jinninta ta fi damunta, dama ita ba irin mutanen nan ne masu daukan wata Aba wai ita soyaya da mahimmanci ba, tun a lokacin da ta so yin soyaya da wani saurayi a aanguwarsu Mama ta zaunar da ita ta yi mata karatun ta nutsu ta wanke mata kwakwaluwa tassssss fa sanar mata irin soyayar nan ta masu gata ce, ba irinta ba wace ta ta fara irgen dangi ta isa ta kawo a yi kashi mu raba a biya haya da shinkafa da wuta da ruwa da dan na cefane, sai ta watsar take tafiyar da rayuwarta daidai da zamani, a tafiyarta kuwa babu kalar wanda bata hadu da shi ba, dan akoy wani da ta taba yi saurayi ya dauketa a mota ya nufi hanyar daji da ita wai zasu je su huta, ya rufe ta a mota ya nemi ilata mata budurci da kyar Allah ya kawo wani makiyayi ya kwaceta ya yi mata sumul tamkar ya santa ya fada mata cewar idan saurayin nada laifi ita ta fi shi laifi, kuma ta kula dan ba kulun Allah zai kawo mai kwatarta ba, in dai tace zata yi wannan rayuwar sunnan mutuncinta barare!, ta gani din, ta kuma yarda da maganarsa, dan mutane da yawa da take ganni da mutunci sun fito mata ta bayan gida a lokacin da suka gane gatanta a duniya mai rauni ne, wanda ke iya tsaya mata shi da kansa bai tsayawa kansa ba bale wani, sai su nemi shiga gonar da take ba tasu ba, da yawa ba maganar soyayar a tsakaninsuma sun nuna mata sunna iya yi mata maganin wata damuwa Tata da ta shafi kudi a duniya ta dan lokaci in har zata basu kanta, wannan dalili ya sa itama ta koyi wata irin rayuwa mai wuyar fassara, tana dukan aljihun maza ba sauki, ciki harda balarabenta da take tunanin tana iya aurensa dan ya nuna alamu da yawa dake nunin yana iya zamowa uban marainiya ba tare da ya wulakantata ba, a sanyaye ta jinginar da bayanta jikin gadon dakin tana ta tunanin shin ina Abdul zai shiga? Kar dai wa'inda suka dauki uncle ne suka dauke shi? Ama shi me zai yi masu na anfani ko me ya tare masu? Ya Allah ka tsare min uncle da Abdul a duk inda suke, ka sa a gansu cikin hayacinsu alfarmar mai alfarma a fadarka. Likitocin nan sun gama duba takardun da aka yiwa Aba gwaje gwajen rashin tashinsa, dan tun a kwanaki hudu da faduwar sa aka daina saka masa maganin barcin, sai gashi har yanzu bai farka daga duniyar barcinsa ba, har an saka masa abin ciyar da mutun idan baya cikin duniyar mutane a makogwaronsa ana ciyar da shi da kalar abincin mai ruwa ruwa da kuma karin ruwan dake aiki a jikinsa A lokacin likitan ya nuna dole sai an tafi da Bah asibiti saboda wani gwajin da ba za'a iya kawo na'urar har nan ta yi aiki yadda ake so ba, a dole aka saka aka kawo ambulance ya zamo Hajia na wajen , Hajia A'isha na wajen, wace tun abin nadin nan ta buya bata yarda su hadu da Hajia bale har ta amshi hukuncin da ta tabatar yana jiranta mai zafi daga Hajiar, sai yau da ta ji za'a fita da mai martabar a washe gari sai gata a cikin makusantan sa na kud da kud a tsaye a falon a lokacin da likitan ke ciki yana sake duba shi dan an kawo ambulance din ama ba zai yiwu a fita da shi a yanzu da dare ke shigowa ba , dan yannayin dare da abin hawa ga dajin dake tsakanin asibitin da fadar ba mai kyau bane, sai kawai aka hakura likitan tai kwana wajensa har ya gama abinda yake yi ya yi zaune a dakin sannan YUSUF ya fito ya samu ahalinsa dake jira ya sanar masu da sauki sunna iya tafiya sai gobe za'a kai shi, Daga nan ya kama kujerar Hajia yana turata dan ya kaita bangarenta ne Hajiar ta dago tana dubansa a tausashe ta ce" Kar ka bari Nana ta biyo mu, kuma kar ka bari ta yi tafiya a bayanmu dan Ni ban yarda da ita ba kuma" Komai a kunnayenta, a lokacin kuma ta yi niyar bin nasu ne, sai ta ji kaffafuwanta sun tsayar da ita sakamakon kallon da ya juyo yana yi mata dan ya gane ko ta ji kuwa abinda mahaifiyarta ta fada? Gannin ta ji ya saka shi sakar mata murmushin da ya kayar mata da gaba, dan walahi har cikin kashinta ta ji wani sanyi mai wuya na ratsa ta saboda murmushin nan nasa, dan haka kawai ta ji a ranta ba murmushin alkhairi bane , gashi tunda girman sarauta ta hau kansa ya zame mata kamar wani dodo, har mamakin harshenta take yi a yanzu da take gaza kama sunnansa tashi daya, bayan a da da kai take kiransa dan badangarci da isa sannan ta fada masa abinda ta ga dama Jiki ba karfi ta juya ta bi hanyar nata bangaren , dan a gidan take rayuwa da mijinta wanda da shi da babu du daya, dan babu abinda ya isa ya saka ko ya hanna a gidan sirikansa, zama ne ake yi tamkar itace mijin, shi kuwa matar, kuma mutun ne mai abin hannunsa daidai gwargwado, dan ya fi karfin masara da shinkafa, ama mugun katari ya afko shi da mace irinta , tun yana gannin zai iya tankwasata a hankali, har ta gama tankwasa shi, yana zaune yana raye ko iyayensa in ba su suka zo ba bai cika zuwa ba, kuma lafiyarsa kalau, kawai duniyarsa itace da ƴaƴansu Kafa take jefawa har ta karasa cikin falonta ta nufi kicin da sauri jin kwaramniyar ta yi yawa a ciki dan kamar ana dukan wani abu haka take juyowa Tana shiga ta kwalalo ido sakamakon gannin yarinyarta mace daya cilo wajen frij tana ta ciro abubuwa tana zubarwa da sauri sauri kamar wace ke neman wani abin da ta ajiye "Dayana" ta fada muryarta har kamar tana rawa A firgice Dayanar ta juyo tana ta kokarin murje idannuwanta dan ta ga mahaifiyar Tata da kyau sannan tana jan rigarta dan ta daidaita tsayuwar ta, idannuwanta masu tsarin halitar gidan su YUSUF sun yi luhu luhu sun yi ja na cikin kuwa sun karra girma da duhu, lebenta ya yi Jajajir kana ganninta ka san a bige take dan duk yadda ta so ta daidaita kanta kasawa ta yi sai numfashi take saukewa da karfi dan ta hanna a gane hallin da take ciki Rai bace, murya sama sama mahaifiyarta ta karasa daidai lokacin da RISLAN ya shigo bangaren nasu da hannun yarinyarsa rike a hannunsa ya jiyo Muryar mahaifiyarsa da ta shaki wuyan DAYANA tana fadin" Dan ubanki shaye shayen kika koma? Nace dan ubanki wani abin kika sha kuma?, DAYANA gwara na kashe ki na huta da dan iskan halayar nan da kike yi a duniyar dan ki sakani a uku, gwara in san na kashe ki na huta ya isk........................" Da sauri ya karasa yana kama hannayen mahaifiyarsa ya shiga kwalkwata a raunane sosai yana fadin" Subahanallah, innalilahi Wa inna ilaihi raj'une Mama, dan Allah ki saketa, ki bari kar ki aikata aikin dana sani , kin rike mata wuya sosai fa" Da kyar ya iya kwatar Dayana, ta rarafa a rikice ta hade bayanta jikin frij din kicin din tana ta fitar da harshe tana numfashi da kyar tana murza makogwaronta tana kallon mahaifiyarta Nana ta nunota a kausashe ta ce" Karya kike ki jaza min abin magana again a gidan nan, dama ido a kaina, karya kike yi ki jaza min abinda za'a fita ana zagina, gwara ki san kin bar kasar nan da ranki da na fitar da ke daga duniyar , dan a shirye nake tsaf yakina yanzu na fara, koda ina son ki, koda kina neman nuna min kin fi karfina bakya jin maganata kar ki manta tushe, duk abinda yake kanki daga nawa ya tashi, kai kuwa uban me ka zo min yi gida? Ba na maka iyaka da fada ba marar anfani?" Kai RISLAN ya sada, gabansa na faduwa ya kasa dagowa bale ya amsa Nana ta ja tsaki a juya dan ji take yi kamar zata kifa ta fice da nufin zuwa ta sakarwa kanta ruwa ko zata ji nutsuwa a jikinta kafin ta zauna ta yi tunanin abinda zai fisheta Dayana kuwa yadda ka san mahaukaciya ta shiga wani irin abu kamar tana karatu a makarantar allo tana ta maimaitawa a rikice tana fadin" Bata son shi, saboda shi take yin wannan abin, Ni kuwa ina son shi, kuma koda bata so sai na aure shi, tunda ina son shi, Ni dai so nake yi ya so Ni Ni dinma, ina son shi, shi nake so tun kafin ta sa na fara soyaya da uban Kulsum, ta kuma sa na auri Sarkin yaki, sannan yanzu tace kuma ba zan so shi ba? Babu inda zan je, ina nan, ina gidan nan, sai ya aure Ni!" Tausayi da tarin tsoro suka saka RISLAN jin hawaye na sauka a saman kuncinsa Mikewa ya yi ya kamata ya mikar da ita yana kiran sunnanta, da kyar ta saurara tana kallonsa a tausashe ya ce" Na san kin san me kike yi, kuma kina jina kina gane me nake fada, yanzu Dayana kina tunanin wannan halin da kike neman maidowa rayuwarki wanka kika daina da jimawa ne zai sa ya aureki? Na zata kin ce shisha kadai kike sha, itama ina ta kokari dan ki daina ashe baki daina ba? Dayana kina tunanin namiji ko lalatace ne zai so ajiye uwar iyalinsa lalataciya?, haba Dayanar dad, ke fa ba yarinya bace , zuwa yanzu ya ci ace kin fara gane ba komai ne alkhairi a duniyar bawa ba, kuma tsananta abu ko menene banda abinda ya shafi neman ilimin addinin musulunci bashi da kyau, me yasa zaki yaki kanki da kanki? DAYANA YUSUF fa ba mijin balagazar mace bane, kuma ke kin san ba shine mai halayar da ake masa kallo ba, kuma kin san tushen labarin abinda ke kokarin nutsa shi cikin sabon Allah ko menene, kuma kin sani sarai har yanzu ba'a yi nasarar abinda ake so din ba, shine ke zaki zo ki yi kokarin sake riko sabon Allah din da nufin Allah ya baki abinda kike so? Haba Dayana sai kace wa'inda muka zo wajen da zamu dawama?" Kwarai tana gane yarensa, kuma tana jin komai a kan gaba Hakan ya sa ta fashe da kuka tana jin kamar kanta zai fashe dan abinda ta sha din bai gama sakinta ba, ita ta rasa yaya zata yi da ranta Rabonta da fita daga falon gidansu ta je farfajiyar gidan nan tunda ta samu ta fita ta ganshi da rawani mahaifiyarta ta hannata fita, shin yaya Mama ke so ta yi da ranta ne? Ita bata ga amfanin wannan tsana da Mama ke yiwa wanda ta san ya gama gamawa da zuciyar yarta, koda yake ba wata damuwa kowa ya yi abinda ya ga dama ita abu daya ne ta sani zata hada kayanta ta kaura wajen Hajia, ta san Hajia ba zata koreta ba, matsalar su ita da Mamanta ne ba da su ba!, kuma ta tabata a cen zata samu ya dubeta dan walahi itace matar YUSUF! "Easy Man easy, kana nufin yanzu zaka shiga dajin nan? Haba oga, ka bari su su shiga mana, me yasa zaka shiga saboda wannan casss din da bai shafe ka ba?" ISHAK ke fada cike da mamakin yadda YUSUF ya iya fitowa daga fada cikin normal shiga da rigar dogari a sama, har ya iya fitowa ya zo madaidaicin gidan da Bah ya taba bashi as girft a lokacin da ya ciyo gasar harda tun yana da shekara goma sha biyar, gidan na nan a da haya ake masa daga baya ya bar gidan ana kular masa da shi yana kwana a ciki in kwana ya kama shi a garin Da mai gadin suka gaisa ya shigo ya samu dakarun aminansa masu tsaron gidansa na jeji da manyan mashin din nan na maza na shiga jeji da abun kai da bindiga da dai duk wani abin da ya dace ace an shirya, a ciki kuwa ISHAK na ciki dama dan a nan ya sauka yanzu kuma ai shi zaman garin abokinsa ya kama shi, bai yi tsamanin zuwan shi ba sai ganninsa ya shi ya shigo yana cire rigar jikin nasa ya haura sama ya shige wanka, yana saukowa ya sauko da wani dogon wando baki sidik da riga mai hannaye kannanu wace ta ba damatsunnan hannayensa damar bayana gudum gudum da su, ya sauko yana kiran Taj yana bashi damar shigowa A nan ne ISHAK din ya gane inda suka nufa dan a lokacin ne YUSUF ya tambayi Taj ya tabata numbar ya santa? Domin a dazun numbar wanda ya yi kiran kawai ya ba Zaj yace a yi kiran layin a yi tracer a san inda suke, nan da sati Daya ya bashi, sai gashi Taj din yana fada masa wannan numbar ai ya santa farin sani ma kuwa, wasu yan jagaliya ne, yan kauyen dake kusa da garin da suka waye da shaye shaye, dan sunna shiga birni ne dan siyan kayan maye su dawo , shine yace to kuwa a yau zasu same su su zanta dan Mah ta kwontar da hankalinta a kan rigimar ƙatuwar y'ar nan da ta dasawa wai ko *BABY* ko me? Abu kamar a yi amai dan sam bai hauta ba gaskiya Bindigar da ya daura a damtsen hannunsa ya gyara da kyau ya wurgawa Ishak wayar hannunsa ya masa murmushi ya ce" Ka dan zauna min ina zuwa, in aka ji na fita daga bakinka ne man hakan ba zai birgeni ba ka ji?" Daga haka ya yi ficewarsa ya bar ISHAK tsaye baki bude ya rasa tudun dafawa 🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗 Azl 24 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo ISHAK ya jima a tsayen nan kafin ya kai zaune saman kujerar yana dan shafa gashin kansa irin na samari da suke tarawar nan, duda shekarunsa sun wuce misalin na saurayi normal bai daina tara gashi ba yana askin yan duniya Wayar dake aljihunsa ce ke ta alamun msg na shigowa, msg din kuwa har da gagautawa Janyo wayar ya yi ya duba msg a jejere, gaba daya kuma abu daya msg din yake dauka shine " Na kira ka? " Idannuwansa ya rintse yana jin amsar dake yawo a zuciyarsa wace ya jima da jin haka tun daga lokacin da ya jima tare da shi yake jin haka a ransa.....da kyar ya iya maida amsa da "ina tare da bos!" "Me kuke yi? Ina fatar da zaka zo ka zo masa da abinda ya fi so? " aka maido masa da amsa a abinda bai fi yan sekwani ba Ajiyar zuciya ya ajiye yana jin zafi a zuciyarsa sosai Uhum, dama ace mai wannan farauta ya gane cewar har yanzu ramin da suke ginawa bawan Allahn nan bai samu zurmawa ba ya ba kansa lafiya? Ama lalle su din *AZAL* ne a duniyarsa, dan ko ba komai sun samu galaba daya a cikin dumbin mugun nufinsu a kansa, a yanzu bai san shi me zai kirayi kansa ba a cikin tafiyar nan, sai dai ya sani ya jima da baro layin mutanen nan daga son tura AMININSA a ramin mugunta, har a ransa yake jin baya ra'ayin wannan tafiyar, kuma burinsa Allah ya bashi damar da zai daina A takaice ya bada amsa da "Eh" , sai ya kashe wayar gaba daya ya turata cikin aljihun wandonsa ya ci gaba da zaman jira yana jin tsoron kar dai wani abin ya same shi, karshema dan ya dauke kewa da zulumi sai ya dauki wayarsa ya bugawa NAFISA da ta tafi kauye wajen Kakaninta suka shiga fira sama sama Lalle dajin mai sunnan Daji ne, dan tunda suka shigo shi basu hadu da mutun daya mai rai ba, sai wasu irin shuke shuken da suka ki bada hankalinsu a kai har suka kai wajen da zasu ajiye ababen hawansu da fatan Allah ya sa idan sun dawo su tardo ababen hawan Kasa kasa sosai Taj ya ce" Oga , bani da tabbacin samun su a nan fa, ina kyautata zaton sunna nan din ne duba da yannayin da muke ciki na zafi, dan jejin da suke zama uku ne, yanzun zafi ne sukan zo nan cikin dare tare da babys din su" Gadanga ne ya amshe da fadin" kwarai bosss, ama ina kyautata zaton samun cika a nan wajajen dan ya kwana biyu bai shiga birni ba, na tabata yana neman kudi ne, nan din kuwa makwoncin shege ne, shi yasa nace mu je a kasa dan na san hanyar bi wace ba za'a zagayemu bamu shirya ba!" Murmushi YUSUF ya yi ya basu dama suka shiga tafia da dan gudu gudu da hannanenyu suke magana tunda suka shigo wajen da basa so a gane sun tunkaro taron da suke hangen wuta irin ta karraruwa na tashi da kidan kalangu ga hayaki na tashi dan tun daga nesa in dai hancinka bai saba jin kaurin hayaki ba tsaf zaka kasa tunkarar wajen Tun daga wannan warin hayakin YUSUF ya rayawa kansa ba taron komai bane sai na yan jagaliyan yara masu shaye shaye, dan kuwa ya tabata in har taron nan na wani jijigegen dan ta'adda ne da ba zai yi wannan shagalar ba ace har a zo inda yake bai ankara ba yana shirme?, ai manyan yan fashi da makami sun jima da daina kwalewa cikin dare a labe a daji, sukan kwale a cikin iyalansu a lokacin da suka yi niya ta yadda ba za'a ritsasu ba, sai ya ji dama ya ji maganar gadanga da yace masa ya bari su je su gane masa ama ya kiya , koda yake shi dinma yana so ya dan ware hannayensa ne Alamun da Taj ya yi kan zai fara zagayawa ta wajen da yake kyautata zaton uban yan iskan na nan ya saka su su kuwa bi ta gaba Da sanda Taj ya karasa ta bayan wanda ke zaune saman kujera gabansa zagaye da kayan makuwa da yan mata cikin shiga ta kannanun kaya sunna ta shegantaka a tsakaninsu ya samu ya dago ya damki wuyansa ya dago shi hadi da mikar da shi tsaye Lokaci daya yan matan suka saka ihu, hakan ya sa samarin dake tare kowa neman wawurar mabuginsa dan basa harbi domin karar bindiga na iya ankarar da mutane wajen zaman nan nasu wanda suke kauna sosai dan tarin ni'imar wajen na shuke shuke da kuma tsoron shigarsa da ake yi dan ana cewa jeji ne mai dauke da aljannu da kuma macizai, dan ko yan kauyen dake makotaka da wajen sunna tsoron shigowarsa shi yasa du suka saye yan farautar kauyen suka daina farauta a jejin sai wani jeji daban Har ga Allah YUSUF sai da ya ji mema ya kawo shi nan to? Abin na yara kawai ya gani dan a tunanin sakarkarin Yaren nan zasu shigo wajen nan ba bindiga ne? Wani tsagera irin na hannun damar ogan ne ya nufo shi a haukace da wuka sharbebiya yana ta wani dire dire irin kwararan nan ne, ya kyale shi sai da ya matse masa waje sosai ya karbe wukar tashi da wajen fadinta ya kasa masa mari da ita sannan ya cira shi ya makawa sauran dake kokarin yin ayari dan su rufa masu Da gagawa ya ciro bindigarsa ya dagata sama da nufin harbawa A rikice ogan nasu dake hannun Taj ya ringa ihun kowa ya tsaya kar ya yi harbi, basa son harbi, kar ya yi harbi basa son karan bindiga! Da mamaki kadan YUSUF yake son ganewa, da gudu gudu Gadanga ya sanar masa ai basa son a gane wajen ne dan waje ne da suke da sirika a boye sosai da kuma wajen hutawarsu, harta mutane idan sun kama a nan suke boye su Hakan da ya ji ya saka shi gane lagonsu a fili da kuma yarda cewar lalle kannanun yan iska ne dake iya zama manyan yan iska nan gaba, dan manyan ai basa tsayar da wajen zama guda daya saboda tsaro, dan zama a waje guda ai hatsari ne ga mai laifi Bai ajiye bindigarsa ba dan kar yara su ritsa kato har ya karasa wajen ogan nasu dake ta tambayar su wanene su me suke so? Me suka masu? A daken da yakan yiwa duk wani bayan Mah da Bah magana ya ce" Dan sakar masa wuya Taj" Taj ya dan sassauta masa rikon, ama bai sake shi ba dan ko ba komai shine baban malamin su, Gadanga kuwa rike yake da tasa bindigar hankalinsa a kan kowa dan gudun kar a yi ba dadi Kallon YUSUF yake yana magana a ransa yana ƙaryata tunaninsa, dan a ganninsa an ce fa Sarkin gidan mashaya ya zama sarki me zai kawo shi nan? Duba da yannayin sarautar garinsu ba karamar sarauta bace, ama kuwa da shi din ne da ya ji dadin ganninsa dan a duniya yana girmama mutumen nan, sun sha shiga basu da ko sisi ya dauki nauyin su harda guzurinsu fa, ai baba sunna jiran ranar da za'a basu damar su kai ziyara fada Allah za'a sha shagali dan sai sun yi masa yar karya karya ta musamman "Akoy wani mutun dake hannunka, wanda ya fito daga masalaci ka kama shi da kudi a hannunsa, mai sunna Umar, ka turawa iyalansa suturarsa da komai, ka bani shi ka janye duk wata alaƙa tsakanin ka da shi da iyalinsa!" YUSUF ya fada a kausashe yana dubansa Da yannayin son kawo raini ya ce" Ban gane ba, a kan aikina fa nake, ka san me ya hadani da shi,? Kudi nake binsa a gidan giya ya hadu da Ni ya ranci kudadena karshema yace zai shuna Ni in ban bashi lafiya ba, na jima ina dakonshi sai da aka kwana biyu na samu nasara na cafke shi, shine zaka ce na baka shi? " Taj ya saka bayan bindigarsa ya maka masa a keyarsa da hargagi ya ce" Kai dan ubanka daidaita muryarka karamin shege, ubanka ne wannan in a wani fanni ka dauko takamarka, ka san waye Ni kuwa? ....." a haukace Taj ya ja hular fuskarsa fuskarsa ta bayyana a gaban shugaban yan ta'addan, lokaci daya YUSUF ya dafe goshi yana kallon Taj da irin yadda shugaban yan ta'addan ya rikice yana juye juye a rikice ya ce" Oga Taj innuwar Sarkin gida in an ganka an ga sarki YUSUF gagara gagarare, Allah ya sa ba rashin jina ya sa na yiwa ubana rashin da'a ba!" Taj zai kuma yin magana YUSUF da ya rasa to su kuwa a ina suka san shi ya masa alamun kar ya saki su gane shi ne, sai kawai Taj ya ce" Sakon da muka zo amsa zaka bamu ka kuma saki wa'inda ke hannunka, ka san Allah in ka yi wasa tsaf zan yi maka jagaliyanci in kai karar ka gaban Oga bossss, dan ka fara kawo raini fa!" Da gagawa ya ringa gyara rigarsa da ya sake shi gannin fadan ashe na cikin gida ne ya yiwa yaronsa ihu da karfi yace" Kai dan ubanka fitar da mutanen nan" Sannan ya maido dubansa kan Taj ya ce" Taj, kai ka san bana kisa , ban taba kisa ba a harkar neman nan, ka san manyan basa bamu aiki, shine muke dan samowa ta wannan hanyar ama dan Allah tsakaninmu ne ka san fa yanzu oga ba zai iya saurara mana ba duba da ya zama uban kowa ko?" Shi dai YUSUF magana ya ki yi, dan tsaf ya san a yanzu in ya yi magana yana iya gane shi, sai kawai yake biye da su kamar ba shi ba har aka fitar da mutane su uku cif, gaba dayansu maza ne, daya ne alamun a jigace yake dan ko tafia kasawa ya yi jikinsa du a kumbure babu wajen da ba rauni a jikinsa, rigar jikinsa wata jalabiya ce mai dati da wani irin wando wanda du a cicire kana gani ka san ba suturarsa bace a jikinsa Da kyar ya iya matse muryarsa yana kallonsu ya ce" Ina Umar din?" Da hannu ya nuna shi Yana sake tsare Yusuf da kallo dan gaba daya wannan din ya kasa gane ko waye kuma sai yake tunanin ko dai ko dai? "Ka maida kowane gidansu, ka bamu shi din,........ka maida kowane nace gidan su, kuma ka bamu shi din, in dai da gaske kake rashin sana'a ta saka ka wannan aikin ka zo fada mu zauna, idan wasa kake yi kuma na yi maka alkawarin zamowa abokin gabarka, yadda kake satar mutane sai na sace ka!" YUSUF ya fada a kausashe bayan ya dan bude hular fuskarsa sun yi ido cikin ido, dan takaicinsa ya ji ya kama shi Da hannu ya masu alamun su tafi da Umar din sannan ya cire abinda yake bakin bindigarsa mai hanna bindigar yin kuka da karfi ya dagata sama ya yi harbi har sau biyar da ita , harbin da ya hargitsa mutanen wajen hatta Umar ya zube a summe dan shi ya zata yau kuma kashe shi za'a yi tunda sun yi ta kiran layin da suka kai wayar ba'a dagawa kuma sun samo numbar maman Salaha sun ce sun yi kira wata yarinya ta daga ta zazzage su, lalle zasu kashe shi a madadin kudin da bai taka kara ya karya ba, kudin giyar da ya sha ta fitar da shi a hayacinsa ba ta saka shi aikata aikin alkhairi ba, lalle ya karra tsinewa wannan rayuwa ya yi Allah wadai da ita, idan yana tuna halin da Rauda zata shiga sai ya ji kamar ya yi ta kuka da ihu, shi kam me zai ce ya zama a duniyar ta? Matsalar ta da damuwarta, bai tsinana mata komai ba sai tashin hankali a gidan duniya Harbin bindigar nan ya rikita kowa har ya zamo bai ga wucewar su YUSUF ba domin a rikice duk wani dake wajen ya shiga wawurar kayansa dan guduwa domin sojan Nijar ba abin wasa bane idan ka yarda ko takalmin ka ka bari wani ya gane naka ne ka fito kuma ka bayana shikenan sai yadda Allah ya yi da kai, shi yasa du suka tsorata suka ringa guduwa ciki harda abokanan shashancin nasa, domin dama iya shegen bai gama bin jinnin jikinsu ba, ana yi ne dan an dandani shaye shaye wanda dama daga kadan din ake zama manya manyan, A saman babur din daure yake da shi a jikinsa a summe suka nufi garinsa direct ya wuce ofishin yan sanda Yana zuwa aka bude masa get aka zo da gagawa aka kama Umar dake summe aka yi cen bangaren asibitinsu da shi sannan ya wuce ciki wajen da baban su ke jiransa a tsaye Yana shiga da mamaki sosai ya ce" Wai dan Allah da gaske kai ne?" YUSUF ya yi murmushi yana cire hular fuskarsa ya bashi hannu suka gaisa da kula ya ce" Abokina ka ɗan daga kafa kadan kafin ku je jejin nan, saboda ina son basu dama kankannuwa , an san ko su waye idan abinda nake son yi bai samu ba zamu bi su daya bayan daya mu kame su" "In sha Allah namiji, ama ka mana garage gaskiya, ka daina dan idan wani abin ya same ka yanzu ai muna cikin kwaramniya kaima" Murmushi Yusuf ya yi ya masa alamun ya wuce, ya fito yana biye da shi har wajen babur din, ya bar Gadanga a wajen Umar suka wuce gidansa dan ya maida kayan nan ya koma masarauta Kafin Yusuf ya koma masarauta ya cika dare sosai yana zuwa ya sake saka kayansa ya fito ya nufi bangaren su ya shige ya karasa dakinsa ya shige wanka, yana fitowa ya gabatar da nafilar da ya yiwa kansa alkawarin ciwo kawai zai hanna shi yi , ciwonma mai tsanani ya yi adu'o'insa sannan ya kwonta yana tunanin ta yiwu Mah na cen ta kasa barci dan yau ya hannata kwana wajen Bah tunda likitansa na nan, Murmushi ya yi yana mamakin soyayar mutanen nan, wato mahaifiyarsa da mahaifinsa, yana masu addu'a da fatan alkhairi a rayuwa barci ya dauke shi Washe gari tunda duku duku aka tafi da Bah, cikin yan rakiyarsa da Hajia da Mah da kuma Yusuf, kafin gari ya waye tarrrr sun dawo saboda asibitin ba wace ake barin majinyata bace, kuma ga likitansa nan da ya zo dominsa kawai yana tare da shi tsakaninsu da shi sai addu'a da fatan Allah ya tashe shi lafiya sai ziyara da zasu ringa kai masa da dare kadai na minti talatin har Allah ya tashi kafadunsa A wannan ranar wajen karfe goma babu kowa dake gilmawa a falo sai Mah da Rauda da Salima dake kicin sunna taya Mah girki saboda Hajia da MALIK da wani mutun mai zane na falon zaune sunna zanen tsarin ginin da za'a maida masarautar , YUSUF din sanye da pyjamins masu ruwan kalar blue da suka jiza sosai, riga da wando masu santsin nan, kansa ko hula babu yana saman kujera ƙafarsa daya tankwashe dayar a kasa yana kallon yadda mai zannen nan ke nake basira yana ta zanen bangarensa wai A daidai lokacin da Mah ta fito dauke da dan karamin plate dauke da bitar shayinsa da yan kofunna na kwalba, bayanta RAUDA ce rike da plate baba dauke da manyan kuloli, sai SALIMA itama dauke da manyan kulolin , a daidai lokacin ne Hajia ke dan rage girman idannuwanta tana kallon zannen ta ce" Malik, bangaren mata fa? Kwaya nawa za'a yi?" Yana kallon Mah ya mike ya amshi abinda yake hannunsa a tausashe sosai ya furta" HUDU " ba wani damuwa ko wani abin da zai dan dakatar da shi ya juyo sai ya ga sun zuba masa ido da Mah din, da Hajiar harda Salima, ciki RAUDA ce kawai ko kallonsa bata yi ba ta ajiye kayan abincin nan ta mike ta nufi kicin ta gabansu bata cewa kowa komai ba har sai da ta shige ya dan lura da ya bita da kallo ya dauke dubansa a lokacin da ta dawo dauke da wasu kayan abincin kasa kasa ya ce" Jiya fa, an ga baban yarinyar nan!" Da sauri RAUDA ta dago idannuwanta ta sauke su cikin nasa, shi dinma a lokacin ita din yake kallo, shi kuwa gashin idannuwanta yake son gane wai yaya ake yi kulun suke a jike? Kukan dai ne Allah ya sa ta kware a shi ko menene? , ita kuma fuskarta lokaci daya ta ringa bada wani annuri ta bude bakinta tana kallonsa, a gaban Hajia wace tun maganar mata hudu ya sakata yi mata kallon kurame dan son gane jikan nata yaya dai?, da Mah da ta girgiza kai da mamakinsa wai mata hudu ko a ina zai wani yi mata hudun?, sai Salima dake kallon zanen da mai zanen nan ta ce" Dan Allah fa? Uncle dina kake nufin ka gani?, wayo Allahna dan Allah da gaske kake?" Kashhhhhhhhhhh☹️☹️☹️☹️☹️🤗🤗🤗🤗 Azl 25 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo Idannuwansa da take kallo tsai ba gargada ko tsoro ya sakata gane irin kallon da ya yi mata mai tafe da dan kakausar zance wanda ya ankarar da ita a yanzu fa wannan din wanene, idan akace sarki kuwa ko mahaukaci ya san me ake nufi A hankali ta shiga risinar da nata idannuwan a ranta tana ayana' Sai kace wace na yi sabo ji yadda kakarsa ke hararena dan Allah, ita kuma Salima ta wani wangale baki kamar mutum zai fada ciki!' Kayan ta kai ta ajiye ta koma kicin din ta zauna sai turo baki take yi,a ganninta wannan sam ba adalci bane, yaya zai fara mata magana mai mahimmanci ya wani gimtse dan daukan alhaki? Ita fa dama tunda ta ganshi ta san mutumen nan zai yi daukan alhaki, da wasu idannuwansa tamkar na Sarkin kwartaye! A tsayen nan da yake bai koma ya zauna ba sai da ta bacewa ganninsa sannan ya zauna daf da Hajia wace ranta ke mugun bace ta kalli Mah da ta yi summar tsaye, ba dan komai ba sai dan a gaban Hajia aka fadi haka, in daga su sai su ne ai zasu waske ne su bada hakuri ita da yarta, ama a yanzun bata san me zata ce dan su kwaci kansu ba Hajia rai bace ta ce" Dama wace kike rikon nan bata da hankali?" Mah ta sake sada kanta, a sanyaye sosai ta ce" Ki yi hakuri Hajiya, yarinta ce" Hajia ta dauke kai tana sauke hatatarta a saman Salima, da sauri ta bar wajen itama ta koma kicin din , Hajia ta ce" ta wuce misalin yarinta tunda ba yarinya mai shekaru uku bace , wannan din raini ne, wanda ba zan dauka ba, dan ko matansa basu isa su yi irin maganar nan da shi haka ba bale wata wai BARE!" Mah ta sake sada kai a tausashe ta furta" A yi hakuri in sha Allah ba zata kuma ba" Shi kuwa Hajiar ya zubawa ido, har sai da ta juyo dan ta sake tambayarsa maganar mata hudu ta ga irin kallon da yake yi mata ta dauke kanta, dan ta sani sarai saboda ta yiwa mahaifiyarsa magana da zafi zafi ne zai sauke a kanta, ita kuwa sai dai ya yi hakuri a gaskiya darajarsa ta fi karfin ta ga irin haka ta yi shiru ko daga wajen uwar tasa ne bale wata wai y'ar riko Daga nan fa maganar ta cenza salo, domin tunda Hajia ta yi maganar nan sai ya zamo ta bata komai, ya yi mata shiru du tambayar da take masa kan abinda za'a saka masa a zanen sai yace da ita ta yi yadda ya mata ya kame bakinsa yana kallon yadda mahaifiyarsa ke kai kawo Gannin ransa ne ya bace Hajia ta salami mai zanen nan tafe zata tabo shi a idasa daga baya Yana tafia ta dubi YUSUF ta ce" Malik, shikenan ban isa na yiwa mahaifiyarka magana ba? Kennan Ni ba uwa bace a wajenta?" YUSUF ya dubi Hajia da kula sosai ya ce" kin tabata idan kina mata magana a matsayin y'arki kike yi mata ko a matsayin sarakuwarki wace kike mutuntawa kike yi mata?" Hajia ta zuba masa ta kasa cewa komai A hankali ya shafa gashin kansa gannin Mah ta fito dauke da abin spoon a tausashe sosai gannin Mah a wajen dan kar ta dakatar da shi ya ce" Babu ruwanki da gaban wa take, babu ruwanki da me zata ji a zuciyarta, babu ruwanki da Ni tawa zuciyar ta ɗan da ta haifa, idan ta dan bata maki ko wani abu da ya shafe ta ya bata maki zaki yi mata sumul ba daga kafa ba jin nauyi ko gannin darajar ta...." Ya dan dakata dan ya ga Mah ta tsaya tana masa kallon me kake yi haka? Sai dai Mah ta yi hakuri a yau bashi da niyar dakatar da abinda ya fara sai ya kai aya idan ya so in Hajia ta ga zata iya zama ta yi nazari ta yiwa kanta fada ta daina toh, in ta ga ba zata iya ba tabas zai ci gaba da yi mata abinda ya fara ba fashi A tausashensa ya ce" ko ba komai ita din nan mai girmamaki ce, tana girmamaki ne dan kin girmeta kuma kin haifa mata miji har ga ƙaruwar ɗa a tsakani, Hajia mutun ce fa, da zuciya a jikinta, koda ta hanna kanta raina ki, ko rama abinda kike yi mata a duniya a lahira kina da abin kare kanki ne?, yaya kike so ki sameni yadda kike so bayan kina hamayya da abinda na fi so a duniya? Hajia bana hada mahaifiyata da kowa, a kanta kuma ina iya dukawa ko waye dan ta ji sanyi....................., Hajia, dan Allah ki dubeni ki dagawa uwata kafa ki bata lafiya, idan ba zaki iya yin magana da ita a sanyaye ba ki kyaleta, ki bar min ita,a hakan zan fi girmamaki fiye da tunanin ki......Please......." Ya karashe yana kamo hannayen Hajia, wace ta yi tsuru jikinta na daukan nauyi tamkar wace ta sha aiki ta gaji, ita kuwa tarin nauyin yaron ne ke lulubeta, a bayane kuma tana gannin kwarai haka din ne, mahaifinsa fa ya sha kwatanta mata, yakan ce mata Andiya bata taɓa nunawa YUSUF ya tsaneta ba, YUSUF nada muguwar shakuwa da mahaifiyarsa, ko shi yana girmamashi duk irin abinda yake masa ne dan yana gannin yadda yake kula da mahaifiyarsa, ya sha fada mata ta ringa yin hakuri ta ringa kiyaye idannuwan Yusuf idan zata yiwa mahaifiyarsa fada, yana dawowa inda take ne dan ya zame masa dole, ya sha fadin ba shi ba gidan nan, idan mahaifiyarsa ta sako kafa ne yake sakowa koda bai shirya ba A karro na biyu kennan da RAUDA ta sake yi masa kallon tsaf, kallon da bai tafe da jin haushi har sai da Salima ta zungura kafadarta sannan suka wuce da dan sauri suka nufi dakin Mah dauke da kayan karinsu su Dukansu harda su Musulima A dole Mah ta nufi ciki itama dan ba zata so Hajia ta kuma dago da idannuwanta ta ganta a wajen ba, dan tsaf take iya sauke mata abinda jikan ya yi mata a kanta, domin itace kuka dadin hawan Hajia, wani da jan fada wani da shan duka za'a yi a wajen nan ,shi yasa ta nufi dakin Bah ta ja kofar ta shiga tatarar dakin da gyarawa tana dantse lebe da tunanin cikin ya'yan nata biyu waye ya fi ja mata magana a yau? Dayar da ta cewa Sarkin ya rantse a gaban kakarsa ko shi dan neman da yake yiwa kakar kashedi a kanta? Allah shi kyauta Ta dan jima a dakin tana aikinta dan har bayi ta wanke fesssss ta rufo ta kunna gawayi ta saka turaren wuta mai daɗi tana sakawa a lungu da sako na dakin ya shigo da salama hannunsa dauke da plate dauke da abincin ta da ya zubo mata Juyowa Mah ta yi, sunna hada ido ta zabga masa harrara sannan ta dauke kanta harda kyaftu tamkar wace ke nunin da zata kama shi ne Murmushi ya yi ya kai abincin saman dan table din dakin ya ajiye yana kallonta ya ce" Mah, zo ki ci Please" Mah ta juyo ta kalli abincin, ta ajiye burner din ta karaso ta zauna daf da shi ta kai hannunta tana shakunar kuncinsa hadi da hancinsa ta ce" Baka jin magana, uwata sa'ar wasanka ce?" Dan murmushi ya yi ya ki bada amsa dan da haka yanzu zata yi fushi Mah ta bude tana kallon abincin da ya zubo ta yi yar dariya ta ce" Yaushe ne zaka fara samun ziyarar abokanan naka? Ko sai an gama ginin?" Hannayensa ya watsa , masu yi mata alamun shi din da kansa bai sani ba, dan haka sai ta dan gyada kai itama ta shiga cin abincinta hankali kwonce Cen ta koro da ci ta ga yana murmushi hadi da girgiza kai, da kula ta masa alamun lafiya?, sai ya sake girgiza mata kai bai ce da ita komai ba, to me zai ce? Jama'a rana tsaka Mah ta dauko ƙatuwar budurwa ta zo zata ƙaryata shi a cikin gidansu? Wannan abu da me ya yi kama? Rabonsa da ace ya tabatar da maganarsa har ya manta gaskiya, dan ko Bah in dai ya fadi abu yana yarda tunda ya san ba zai masa karya ba ai, rayuwa kennan idan baka mutu ba ka sha kallo Sai da yama liss Mah ta sanarwa RAUDA eh da gaske an ga Bah dinta, sannan ta bata damar ta je gidansu ta sanarwa maman nasu kuma su dawo da bakonta wanda da kyar ta sanarwa Mah ya iso Nijar din kuma yace zai zo bata san yaya zata fada masa tana nan ba, Da kula sosai Mah ta ce" Zaki tafi da ke da Salima ne, idan kun je ki yi kokarin sanarwa bakon inda kike, ki fada masa sak gidanku nan ne, kuma Ni ce mamanki, ki kula, ki kama mutuncin kanki, ko wanene shi in dai da gaske yake ya fara neman izinin ganninki wajen manyanki kafin ku ga junna a ka'idance, a yanzu na baki damar nan ne dan yadda kika kwatanta min darajar da ya baki ya sa shima na bashi darajar gannin y'ata a haka, ki sani kina da daraja wace take tafe da darajaza daga bakin lokacin da kika amsa sunnan y'ata, ki kula da mutuncinki, ki kula da mutuncinki, idan ya baki wani kyauta kar ki amsa ko menene , ki bari sai kin sanar a gida kin ji?" RAUDA na tsaye ne Salima na ja mata zif din Abayar da ta saka, dan irin egypcien Abayar nan ne budadu masu kyau da tsari, Mah na yi mata maganar dan idan sun tafi itama zasu fita ne da su Hajia matan Bah gaba dayansu dan zuwa ganninsa a asibiti Har ga Allah bata san ta shagala da kallon Mah ba sai da Salima ta ankarar da ita sannan ta sada dubanta ta amsa Mah din kafin ta karasa ta yi tsaye wajen turaran wutar da Mah din ta saka masu tana fadin su tabatar sun turaru sannan kar Salima ta yi tuki direba zai kai su ya dawo da su, ƙafarsa kafarsu du inda suka shiga ya bi su Daga haka Mah ta fice , Rauda ta gama tauraruwa ta dauki mayafinta blue mai haske sosai ta yafa a kanta , hakama Salima ta rufa mayafin abayarta sannan suka fice Tunda suka kama hanya Salima ta kula da yannayin sanyin da jikin Rauda ya yi, har ta kasa hakura wajen Danja ta yi mata tambayar abinda yake damunta Da dan murmushi Rauda ta ce" Me kika gani Salima?" Salima ta ce" Na ga daidai lokacin da kika fito daga wanka da yanzu ba daya bane yannayinki, ina fatan lafiyarki kalau?" RAUDA ta yi mata murmushi bata ce mata komai ba har suka karaso kofar gidan suka sauka daga motar direba ya parker yana jiransu, domin bakon Salima ya fi minti talatin a motar a zaune yana jiranta, motar da Salima na gani ta gane ko wace irin mota ce domin Bah ya hau ta, ƴaƴansu ya bashi ita a lokacin da ya sauke su Tunda suka sauka daga motar ya bude ya fito, fuskarsa ke dauke da murmushi yana kallonta har ya karaso inda suke tsaye yana sake sakin fuskarsa da walwala sosai ya ce" ina farin cikin sake gannin ki masoyiyatah" RAUDA ta yi dan murmushi tana dauke dubanta a kansa ta maida kan Salima wace ke yin murmushi tana kallon Balarabe sak abinsa, hausarma gatanan dai, ama zai yi Sa'a Bah gaskiya Da dan murmushi a fuskarta ta furta" Marhaban bika fi'akhi" Murmushi ya yi sosai har kamar ya rungumeta ya yi mata irin gaisuwarsu ta larabawa, ama ta jima da sanar masa ta fi so su kiyaye hakan su yi koyi da abinda addini ya kawo Yana kallonta ya ce" Na gaza hakurin sai gobe na gan ki, ku je cikin mu zauna ko?" Da da ne, zata iya jan shi cikin gidan koda ta shekara bata nan, ko ta je motar tasa su zauna su zanta, ama a yau sai take jin wani iri kamar ba zata iya ba, Saima da ta kalli Salima, sai ta ga kamar wace take mata gargadin zuwa ta shige motarsa Kai ta dauke a tausashe tana kallonsa ta dan langwabar da kanta ta ce" Ka yi hakuri na Barka kana jira, ka san yanzu ina cen gidan.....gidan....." "Gidanmu, take nufi, gidan garin Tsatsunburum, Ni yar uwarta ce, yanzuma mamah ce tace mu zo mu sanar maka, ana son ganninka a fada " Salima ta karɓe zancen, a tausashe ta sanar masa sakon da ta kula Rauda ba zata iya fada ba, dan tunda ta fara maganar nan ta shiga dan juye juye da dan shafa agogon hannunta ta tabata zancen bata gama karbar sa ba sai kawai ita ta sanar Harda ajiyar zuciya Rauda ta sauke dan kuwa Salima ta taimaketa ainun, domin bata san yaya zata fada masa ba, dan kusan duk wani wanda zai fita da ita bayansa ne, shi din ya san komai nata, ciki harda marikiyarta Abdullal Jabar abin ya daure masa kai ainun, sai dai wannan magana ta ana son ganninsa a fada ta saka shi rikicewa da farin ciki, kwarai Allah ya amshi adu'arsa, ga dukkan alamu abinda ya roka kan kar ta wahalar da shi ko ta ki shi Allah ya amsa A hankali ya juya bayan Salima ta sake tabatar masa da maganar da yake tunanin haka ne, cike da shauki da farin ciki, Rauda na biye da shi har kusan motarsa, sannan ya sake juyowa yana kallonta da tarin mutanen dake ta kallonsu ba yaran ba, ba manyan ba ya ce" dama kina da alaka da HONORABLE BELLO?, " RAUDA ta sada idannuwanta, a hankali ta ce " bayan tafiyarka, Allah ya hadani da shi da matarsa da kuma dansa, shine suka daukeni , matarsa tace ita din uwa take a wajena zata rikeni tamkar y'ar da ta haifa, hakama mijinta ya yarda" "Wai kina nufin harda SS YUSUF ?" Ya fada yana zarro idannuwansa cike da mamaki Dan tsaida maganarta ta yi tana kallonsa Sai ya basar, gannin kallon da ta yi masa, ya dawo kan maganar da ta fada din ya ba abin mahimmanci sosai Kwarai ya ga cenji, domin babu irin yadda bai yi ba kan ta tsaya ta amshi tsarabarta ta nuna an hannata sai ta tambaya a gida, karshe dai suka rabu da cewar gobe da dare zai je ta sanar a gidan nasu , ya juya ya tafi yana jin kwarai nutsuwa na shigarsa, a yanzu ya san idan ya buga da karfi Rauda tashi ce , burinsa zai cika kwana kusa kennan? Allah kennan mai yadda ya so da bawansa a lokacin da ya so Tana juyowa idannuwanta suka sauka kan Salaha dake tsaye a dokin kofar gidan, jikinta sanye da wani zani baki wanda a ido kawai idan ka kalla ka san ya yi dati, rigarta kuwa kamar irin kannanun rigar nan da ake sakawa a ciki ne du ga nono nan ya bayyanar da kansa sai wani dan kwalin atampa ta yafa tana kallon Raudar da bakonta Da sauri ta koma gidan gannin Raudar ta nufi gidan da wata bakuwa Tana shiga da karfi ta ce" Mama, walahi gatanan shegiyar ta dawo, an gama yawon ta zubar din, kin ga balaraben da ya ajiye ta? Ni dai ko randa ta taba ba zan sha ruwan randar ba, kar na gogi kanjamau, kin ga wai yadda ta karra fari? Ta yiwu ita ta sake maki miji kina nan kina kuka a banza a wofi , ai na fada maki ki daina kukan nan tunda kin dauko Abdul zata zo ne!" Turus RAUDA ta yi jin magangannun da Salaha ke yi Ai kau idannuwanta suka sauka a kan Abdul dake zaune gaban pampo yana wanke wanken kwanoni, kana gani ka san ba a hayacinsa yake ba, tsoro ne fal a fuskarsa kuma wankewar sai yi yake kamar an aiko shi A raunane sosai ta ce" Abdul" Ya ji ta fa, ama yaron nan ya gaza waigowa dan a tunaninsa ba ita din bace kunnayensa ke masa gizo "Munafuka, annamimiya, yau sako ya je maki baya nan kin zo nan nemansa ko? Kwarai ni na dauke shi ko zaki tuna da ubanki wanda ya rike ki ki zo ki nemo shi, in banda rayuwa irin ta wanda baida imani ke har kya manta Umaru? Ko fitar nan da ya yi ai sanadiyar ki ne, dan kin kawo masa kudin karuwanci gida, shine zaki tafi ki yi kwonciyarki ance a masarauta ko? Sai ki zo ki samo min mijina idan ya so ki biya Ni bashin da nake bin ki sannan ki dauki wancen mahaukacin ,dama rikonsa sai ke ai!" Bata tsaya bi ta kan magangannunsu ba, magangannun da suka saka Salima daskarewa a waje daya cike da tsoro da mamaki, idannuwanta rufe ta karasa wajen da Abdul yake da sauri ta dago dago shi, jikinsa da dati da abin fitsari da abin miya gaja gaja ta rungume shi a jikinta a birkice murya a rarrabe tana fadin" Azl 26 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo Tana fadin " Abdul, Abdul, Abdul Nine, auntynka ne, kalleni Nine fa" Tunda ta rungume shi, ya shiga maganganu hadi da kuka, magangannu irin wa'inda mutun kan tarawa idan wani wanda ke hanawa a wulakantashi baya nan aka wulakanta shi idan ya dawo dan ya sanar masa Ido a rufe hawaye a fuskarsa yake fadin" Auntyna, auntyna ko? Sai ta zane ku, ku dukan ku, idan ta zo sai na fada mata Salaha ta zane Ni, ta hanna min tuwo, ta hanna Ni zuwa makaranta, dan ta ce na mata wanki nace ban iya ba ta saka na yi ta zane Ni, ta saka na yi shara, Abdul bai iya komai ba ama tace sai na yi sai na yi wanke wanke, har na kone hannuna da mama tace sai na hura wuta, sun ce Abdul maye ne sai kallon mutane, bayan auntyna tace Ni ba maye bane, sun ce wai sai sun yankani idan baki zo ba, kin gansu sun doke Ni, sun rufe daki sun barni na kwana a waje , ina tsoro ina tsoro ina tsoro......" Sai kawai RAUDA ta fashe da kuka, a rikice ta dago tana kallon Mama wace ta karaso tana son kwalkwatar Abdul dan ba zata taba bari ta tafi da shi ba, domin idan ta tafi da shi ta san shikenan kuma labarin mijinta ba zata kuma ji ba, ita kuma walahi wannan abin sai ya haukatata, rashin Umar tuni yana daf da zautar da ita, A rikice ido a kausashe Rauda ta yi mata nuni da yar yatsarta ta ce" idan kika kuskura kika taba hannunsa , yau sai na yi kason ki!" Ido Mama ta kwalalo tana ja baya tana kallonta, dan tunda suke, tunda Allah ya hada zamansu bata taba yi mata magana ido cikin ido da tabbacin furucinsta irin na yau ba, duk irin yadda kirjinta je hayaki a kan maganar mijinta sai ta kasa kwatar yaron da take gannin shi kadai ne hanyar da zata rika ta rike wuyan RAUDA sai yadda ta yi da ita ba RAUDA ta dago fuskarsa tana kallonsa ta ce" In zane su? Kana so in zane su?" Abdul ya ringa gyada kansa yana kuka yace " Aunty? Ke ce ko? Aunty ki zane Salaha, kin ji? Tace Ni ne wai mai kama da aljannu, kuma tace min mahaukaci......" Ai bai gama rufe bakinsa ba ta maida shi bayanta a guje ta ridi Salaha Kafin Salaha ta samu ta gudu daki Rauda ta yi mata rikon da ta fi jin tsoro, ta rike mata wuya daf ta watsota waje Salima ta zarro ido abin na neman fin karfin ta tana neman kiran sunnan RAUDA wace ta shake wuyan Salaha sosai ta sake zarro ido gannin Mama ta dauko katon ludayin miya irin tafkeken nan ta daga ta makawa RAUDA shi a bayan kanta Ihu Salima ta saka, da gudu ta nufo Mama tana neman rike ludayin ama sai da Mama ta sake makawa RAUDA shi tana fadin" Na maki alkawarin nice ajalinki, sai na kashe ki!, ba kin samu gidan sarauta kin labe ba? Dole zaki dawo inda nake ki nemo mana abinci ko ciyar da mu , dole zaki fito ki nemo min mijina , munafuka algunguma shegiya mai tafe da *AZAL* a duk inda kika shiga, iyayenki dan sun haife ko masifa kala kala sai da suka shige rami gaba dayansu koka huta, Ni da aka kawowa ke gashinan kulun cikin balaki nake karshe wanda ya dauko kin zaki jawa a rasa inda yake?, karya kike yi mai kama da kulba sai dai na kashe ki na kashe banza!" A rikice Salima ta yi waje, dan abin ya fi karfin ta, kuma abinda ya bata tsoro du irin ihun da suke yi makota babu wanda ya leko ko wa'inda ke waje babu wanda ya shigo Da gudu ta karasa wajen direba jikinta ma rawa ta shiga nuna masa tana haki tana fada masa lokaci daya kuma tana fadin" Ta kashe RAUDA, ta kashe ta, innalilahi wa inna ilaihi raj'une, ka kira police, ka sanarwa mai martaba kar Mah ta ji, kar ka sanarwa Mah!" Magana take yi hankali tashe tana son juyawa gidan da sauri direban YUSUF ya fito daga motar ikon sauri ya ce" Hajia, ki dan tsaya kar k8 shiga bari na je" Kana gannin yadda yake magana ka san irin mutanan nan ne da basa tsoron a mutu, direbansa ne wanda ke kai Mah anguwa idan baya nan, mutumensa ne da dalili ya haɗa har ya dauke shi aiki Yana fada ya nufi gidan da sauri yana kautar da mutanen dake tsaitsaye, ita kuma tana biye da shi a guje dan gaba daya anguwar ta shiga bata tsoro Salaha ya fara ganni rigar dake jikinta ta yage sosai, ama ba ta kirjinta dake fili take ba, sai kakari take ta cuje rufar da ta yiwa kanta, gashin kan a tsaitsaye sai kwalalo ido take tana cenza waje, sket din jikinta kuwa harda jika kamar wace ta zabga fitsarin kwonce "Ina Hajiar?" Ya fada murya a kausashe yana kallon Mama, wace ke haki sai yade yaden magana take yi kan ta ga ubanda zai fitar da RAUDA domin bayan ta sumar da Raudar kama kaffafuwanta ta yi ta ja ta da kyar ta kaita falo, sannan ta hankada keyar Abdul ya je ya rukunkumeta yana ihun kuka , a nan ne Salaha ta mike kamar zata mutu ta sace wayarta dake yashe a nan ta boye a jikinta sannan ta ci gaba da murzar jikinta dan walahi ta shaku iya shakuwa "Wace Hajia?" Mama ta fada tana kame kame dan daga yannayin tsayuwarsa ta san yana iya yi mata aikin gajanci la'ada waje Tsaki ya ja gannin matar fa kamar wata cika ce Walahi, sai kawai ya shigo da kyau ya nemi zagayeta dan shiga dakin lokaci daya yana neman layin YUSUF Har zai shiga ya dan juyo gannin ta dauko ludayin nata ya dan zuba mata ido sannan ya kalli Salaha da Salima da suka yi zuru zuru sunna kallonsa Alamu ya masu na su dan dakata , daga tsayen da yake ya risinar da kansa, ya jimke hannunsa da girmamawa sosai ya furta" Barka da warhaka Uban mai uba, marar ubanma kaine ubansa, Barka da warhaka ja gaba ikon Allah, Barka da warhaka dashen Allah, rubutace kake babu wanda zai goge, Allah ne ya nadaka uban gidana ba wani dan Adam ba, dama ina kira ne dan ya kama dole na yi kiran" YUSUF ya girgiza kansa, ya fara gane abubuwan nan da da wahala a bashi lafiya da su, wato kirari kirarin nan sai kawai ya share shi , a hankali ya furta" Lafiya?" "Dama su Hajia da na kawo ne aka samu matsala, dan inaga a summe take sosai, matar da muka zo gidanta ne ta shinfida mata koshiyar girki!" Ya fada da irin Muryar nan ta daba, yana sake gyara yannayinsa tamkar a gaban YUSUF din yake YUSUF ya yi shiru yana tunanin ikon Allahn nan, kai jama'a summe kuma?, ga Mah a cikin zuciyarsa wace tashi daya ya yi tunanin idan har ta ji ai itama tana iya sumewar A kame ya furta" ka dawo da ita yanzu yanzu, a shigar da ita ciki kafin su Mah su dawo likita zata yi jiran ku" Daga haka YUSUF ya katse kiran nan ya shiga kiran layin likitarsu ta familly A dayan bangaren kuwa ana katsewa ya mayar da wayar aljihun rigarsa ya juya da nufin shigar, sai ya ga still Mama na son yi masa ganganci Juyowa ya sake yi yana murmushin da ya kashe zuciyar Salaha dukda halin da take ciki ta yi mutuwar tsaye tana kallonsa Yana kallonta ya ce" Hajia yawa ne walahi, idan kika gwada ba zai haifar maki da d'a mai ido ba, dan tsaf zan moda maki shi a Keya numfashi ya dauke a kamani, ki dan bari mana na gama aikin oga dan har ga Allah mu yan a mutunsa ne, oya bani hanya dan dole na dauko Hajia!" Yana gama fadi ya shige ciki , ya tarda Abdul zuwa yanzu muryarsa ta gama disashewa ta yi kwonce jikin RAUDA yana ta kuka mai fitar da hawaye ama babu amo Dan zuba masa ido yayi yana mamakin meye ya haɗa matar nan da mutanen nan masu salihan fuskoki?, yaron nan ya bashi tausayi ainun, hakan ya sa da ya talaba RAUDA Abdul ya riketa tam yana kukan kar a tafi da ita ya fara tiso shi gaba suka fito da ƙafarsa ya nemi hangaje Mama da ta so riko Abdul din , da idannuwansa kuwa ya mata alamun yana iya daka mata kafa , hakan ya sa Mama kwasar kururuwa tana fadin yan anguwa su taimaketa kwarton RAUDA ne ya zo ya dauki harda Abdul marayan Allah zai tafi da su duka su kwato mata su, ama yan anguwa suka ki bin shi har Salima ta bude masa bayan mota ya saka RAUDA Abdul ya shige yana sake riko hannunta na dama dake yarfe, shi kuwa ya shige gaba Salima ta shige bayan itama ya tada motar ya figeta ya fice a anguwar Sosai mama ke ihun kuka, kukan da take yi na yanzu mai shiga zuciyarta ne yana tarwatsa duk wani tunanin gannin mijinta da ta yi a kwana kusa, dan gani take idan har aka tafi da RAUDA da kuma Abdul shikenan babu mai nemo mata Umaru , hakan na nufin ya mutu bata ga gawarsa ba, hakan na nufin zawarci ya kamata da ciyar da kai da biyan haya, hakan na nufin rikon Yar nan cilo ya dawo hannunta gaba da baya, hakan na nufin ko a koma saide saiden abinci a bakin titi ko kuma a koma kauye in dai ana so a rayu? Ina , ba zai taba yiwuwa ba, walahi har garin nan da Rauda take sai ta bi ta dan itace kadai zata iya nemo mata mijinta a garin nan! Tana komawa ta tarda Salaha zaune ta tafka tagumi da hannayenta bibiyu tana kallon kofar da Maman nata ta fita Mama ta karaso inda take da tausayinta tana share hawaye ta ce" Salaha, kema kin fara shiga tunanin mahaifin naki yanzu ko? Ko ta jiyatar da ke ne? Tashi ki yi wanka ki je chemis ga yan cenjina nan a baki magani kar aje ta maki mugun rauni kin ji?" Salaha ta cire tagumin da ta yi ta zubawa mahaifiyarta ido tana tunanin yaya zata yi da matar nan dake son saka mata hawan jini kiri kiri? Da wata murya ta rashin kunya, wace du dan arziki ba zai yiwa koda yayansa ne magana a haka ba bale mahaifiya, mutun mai daraja a duniyar bawa, Salaha ta budi baki tana kallonta ta ce" Yanzu ke mama a duniyar nan du abinda ya nufo Ni na rufin asiri sai kin saka kafa kin shure? Da idannuwana nake miki alamun ki barshi ya dauketa su tafi, ki barshi mama ama kika ware murya kika tatare zani kike ihu kan wani mijinki da ya tsufa ya gama bugawa? Haba dan Allah to wai Ni ya ake so na yi da raina ne? Daga kin ga na gilma ki isheni in yi wanka, in wanke kafa in wanke pant in wanke baki in wanke kai, bayan fatar nan in aka cika yi mata iya yi tsaf zata tsofe ta bar kai ba komai? Hana dan Allah wankan nan duka duka yau kwana uku rabona da in yi, kuma na fada maki ki bani lafiya in na gama al'adata nake son haɗawa harda wankin kan na yi ko? Ama kiri kiri mama kike ce min in yi wanka? Yanzu wannan din da kika yiwa haka Ni ai ina ganninsa na ji na kamu da son sa, yanzu in na nemo shi na fada masa yace ba zai iya yi ba saboda uwata me kike so nace maki? Gaskiya a ringa yi ana tuna in fa na rasa miji lalacewa zan yi, dan walahi ba zai yiwu in zo in koma zikau ba, ina.....!" Ta karashe tana kade kafarta ta nufi ciki ta yi dakin Rauda dan nemo hijabi mai kyan gani ta fita, domin a yanzu yanzu zata batar da wayar nan ta dan samu kudin da zata fara nemo wannan gayen, kwal uba sak irin gayen da take so take burin aura a rayuwa kennan fa, ita fa in yace Mamanta ce bata masa ba sai ta sayi iyayen karya ya samu ya aureta daga baya ta ringa zuwa wajen mama koda a boye ne! Kumnayen mama suka saurari kalaman yarta ta cikinta, ama zuciyarta ta kasa gaskata mata gaskiyar lamarin A tsugunnen da take, ta kasa mikewa bale har ta iya tarda Salaha dan su yi magana ta gane ko kanta ta buga ta samu tabuwar hankali ne? Har sai da salahar ta fito ta fice a gidan sannan ta iya dagowa tana jin jirri na kwasarta Da kyar take kiran sunnan salahar, ama firrr yarinyar nan ta yi kamar bata ji ta ba ta yi ficewarta gashi kiraye kirayen magariba ake yi yanzun , wasu masallatan har sun shige sallah, gashi anguwar ta ki lafiya yanzu a yi wannan a yi wancen, kar dai Salaha ta haukace ta shiga uku? Wannan tunanin ya saka Mama daukan hijab ta fito tana janyo kofar su ko rufewa da kyau bata yi ba ta shiga bin layi tana haskawa da yar hannu tana neman Salaha, a lokacin da ta fice ne kuma wasu yan samari irin mararsa jin anguwa suka yi wuf suka shige gidan suka shiga yan tatare tataren abubuwan anfani da gagawa suka tattara abinda zasu iya fita da shi suka ficewarsu hankali kwonce! Tafiyar gagawa ya yi domin cikin abinda bai fi minti arba'in ba suka karasa fada kuma ya samu shigewa har cikin fadar har bangaren su YUSUF da motar domin umarnin da ya sake bashi kennan a lokacin da ya yi kiransa ya shaida masa a summe take fa, har yanzu bata dawo hayacinta ba, kuma ta zubar da jinni sosai daga keyarta shi kam abin ya fara bashi tsoro, shine ya saka shi shigowa direct har cikin gidan da motar sannan ya saka shi bi ta baya ya zo har kofar bangarensu ya ja ya tsaya dan dogarai ba zasu barshi shiga get din ba daga nan, domin yanzun tsaron ya ninka na da sosai, yanzu bayan dogarai harda polisawa ke ba fadar tsaro kuma an fi ba wannan wajen tsaron fiye da ko'ina Kasancewar a lokacin yana masalaci sai da suka gama sallar Isha sannan ya fito tare da mutanen dake biye da bayansa suka nufo hanyar gidansu, har sai da suka kusa isowa ya salame su yana shaida masu zai shiga da wuri yau Sai da suka gama kirarinsu yana kallon su suka juya sannan ya shiga takowa a nutse idannuwansa a kan polisan da suke take masa baya wasu daga gabansa, ya girgiza kai a ransa ya furta' Sai kace wa'inda in Allah ya yi wani dan iya shegen zai kashe Ni sun isa su hanna, kawai salon a hanna mutun wali a cikin gida a hanna mutun motsin kirki!' Yana karasowa wajen motar direban ya fito ya duka har kasa hannunsa jimke yana masa kirari mai haɗe da yi masa Barka da karasowa Cikin gundura da magangannun nasa ya ce" Azl 27 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo Cikin gundura da magangannun nasa YUSUF ya ce" tana ciki ne?" Kai ya girgiza da sauri kansa a kasa ya ce" Tana bayan motar, ai baka ce na kaita ciki ba Allah ya karra maka lafiya" Dan tsai ya yi, ya dan dube shi , kasa kasa ya ce" Ka kaita ciki?, dama kai ka dauketan?" Wannan karron dagowa direban ya yi ya dan kalli MALIK, kafin ya maida kansa kasa, da girmamawa sosai ya furta " Allah ya taimakeka, a sume take ne, gashi Hajia ba zata iya daukanta ba, shi yasa na sakata a motar" Kai YUSUF ya dauke yana tabe bakinsa ya nufi motar Salima na ganninsa ta bude bangaren da take zaune kan Rauda saman cinyarta, Abdul kuwa ya kwontar da kansa a kirjinta , gashinta a fili ta cire mata ribom dinta ga jinnin nan har a jikin rigar Salimar da kuma gaban goshinta Wani irin bugawa ya ji zuciyarsa ta yi, hakan ya sa ya dauke dubansa ya kalli direban dake dan nesa kadan , kasa kasan nan sosai ya furta" Ko ta mutu ne?" Da sauri direban ya girgiza kansa ya ce" Wahala ce kawai ta sha, ai abin ba karami bane kuma inaga an shamaceta ne sosai fa" YUSUF ya dauke idannuwansa daga kansa ya sake kallon Salima dake ta share hawaye hannayenta du jinni ne, sannan ya mika hannu ya furta" Bani ky" Ky din motar ya ciro ya duka yana miko masa, ya amsa ya juya yana masa alamun ya tafi da yan yatsunsa sannan ya bude gidan gaban ya shiga hankali kwonce yana jin kamar ya cire rawanin a nan ya ajiye dan yadda yake jin tamkar numfashinsa na masa nauyi, bai san dalili ba, ya dai san kawai yana jin isla na neman yiwa kofofin hancinsa kadan Idannuwa ya sauke kan polise don da ya shige gefen direban yana fadin" Sir ka kawo na yi driving Please" Bai ce masa komai ba ya tada motar ya nufi hanyar get din, sauran suka ringa bin su da gudu, dogaran dake gadi suka bude get din sunna risinawa tare da kirarin da suka saba har motar ta shige gaba daya ta wuce cen gaban kofar shigewa ya parkerta a nan Kashewa ya yi a nutse ya ziro kaffafuwansa ya fito domin tuni police din nan ya bude masa motar Bayan motar da ya kalla ya saka police din budewa sannan ya tsaya yana hankalce da yannayinsa, shi dinma dan tsayawar da ya yi kawai nazarin police din ne yake yi da mamakinsa Uhum ya dan fitar daga kirjinsa yana kallon Salima, wace ke kiciniyar kamo Abdul ama yana girgiza mata kai da nuna mata RAUDA, yaron ya jigata har muryarsa bata fita sai yake yi kamar bebe yana nuna mata A sanyaye ta ce" Abdul, ciki zamu shiga a duba auntynka ka ji? Ka yi shiru hakanan kaima ka ga baka da lafiya ko?" Kai ya ringa gyadawa ya kama hannun da take bashi suka sauko da dan hanzari ta kauce tana rike da hannun Abdul tana so ta ga police din ya yi ya dauko Raudar su shige ta ga ta bude idannuwanta ko hankalinta zai dawo jikinta YUSUF ya dan daga ƙafarsa kadan dan aikata abinda ya yi niya , sai ya ga Police din da sauri yana nade hannun rigarsa ta kaki yana masa alamun ya dakata shi zai daukota ne ai A ransa ya ayana' toh fa' A bayane kuwa sai ya ki dakatawar ya saka hannunsa gashin nan nata dake baje da ya fi bashi haushi , a ganninsa in ta san fadanta zata je yi ta saka hula mana? Yarinya kamar wata kura du in ta fita sai ta daku? Yau dai an sha duka su uwar fada ta yiwu a daina. Gannin police din nan ya bude dayan bangaren ya saka shi zura masa ido, ta wajen inda kaffafuwan uwar Abdul yake ko wa police din ya je, shi kam ta yiwu an hadda shi da tababe kuma, yake ta ayanawa a ransa, kasa kasa ya furta" Bari mana, kar ka dauketa" Dakatawa police din ya yi, har ga Allah bai gane shine zai dauketa ba, shi yasa ya shirya iya shirya wa dan kar ya daukota aje tana da mugun nauyi ta kada kato a shiga uku, sai gani ya yi Sir da alkhyabarsa ya cicibo RAUDA ya mata daukan jaririya domin a hannayensa ya daukota ya juya ya nufi ciki, shi kuwa daga nan ya tattara kakayayakinsu ya ba Salima da ya dakatar sannan ya ja motar ya fice da ita dan sai ya mata sumul zai dawo da ita ya ajiye a muhallin ta sannan ya ba direban dake janta ky dinsa A nutse yake nufar dakin Mah, tunda ya shigo din, likitar kuwa na take masa baya bayan ta risina ta masa Barka da karasowa hannunta rike da jakarsu na likitoci sannan ta bi bayansa kamar yadda ya mata alamu, yan matan dake zaune a falo na biyu kuwa suka yi mutuwar zaune suka bi abinda suke ganni da ido, dan babu wani abinda ya shafe su da reton da hannunta yake yi, abinda idannuwansu suka gane masu shine MALIK dauke da wannan budurwar da Mah ke kira baby, wace Mah ke yawon nuna mata kulawa a gaban kowa, Wada Mah tace y'arta ce bayan iyayensu sun sake tabbatar masu basu san lokacin da ta haife ta ba, ya nufi dakin Mah da ita , likita na biye da su, Salima na dafe mata baya....kusan sai suka rasa abin yi a zaunen nan, domin a dan zaman nan da suka yi sun riga sun fahimci in dai so suke yi su sayi wata zuciyar da zata iya kusanta su da YUSUF sai dai su sayi ta mahaifiyarsa, dan duk irin yadda aka nuna masu mutumen mutumen mata ne, abin na neman gagararsu, dan ko da wasa su dai abin nan bai tabata a kansu ba, sai gani sai hange tsakaninsu da shi, kusanci ko na kwabo sun kasa ciyowa daga fadarsa, ko a yanzun gaba dayansu tsoron karasawar inda yake ya saka su tsayawa da zubawa sarautar Allah ido! Tunda ya bude dakin Mah Musulima ta dago daga vidio call din da take a saman kujera ta ji tamkar zata summa ta zuba masa ido, lokaci daya kuma ta mike tana daukan hijab dinta dake ajiye ta ware shi za saka ta fice a dakin dan tunda ya kalleta sau daya ya ja tunga ta san me hakan yake nufi, a dole ta saka hijab din da aka saka su saka shi dan dole a cikin gidan ta fice tana jin zuciyarta tamkar zata fito daga kirjinta, dan Allah yana ganni ita a zaman nan da farko an nuna mata wannan miji ne da ya dace da duniyarta dan sarautarsa da kudinsa, a hankali ta idasa gane ko bayan su, miji ne da ya dace da ita dan ya isa a so shi, ya haɗa qualities na mamaki, ya kasance jaruminta burinta, mafarkinta, ita fa ta jima da kamuwa da so din da koda bashi da komai tana iya rantsewa cewar zata iya zama da shi, bale ga ya'yan banki ga sarewa jama'a, kwarai a matsayinta Na yar Sarkin kasuwa ya dace ta zama matar MALIK, a nan sarautar zata gama haduwa gaba da baya Direct bakin gadon ya kaita ya shinfidata sannan ya juya ya koma wajen kujerun nan ya zauna yana duban agogonsa da auna lokacin da Mah ke iya shigowa a zuciyarsa Likitar kusan du Salima ta yiwa tambayoyi ita kuwa ta bata amsar gaba daya abinda ta sani dan haka da gagawa ta juyar da RAUDA ta shi bata taimakon da zai taimaketa ta hanyar fara duba ciwon da ya hadasa mata zubar da jinnin nan dan ba sumar ta fi damunta ba , ba kamar ciwon dan in har ya taba wajen da ba'a so dole a kaita asibiti a shiga bincike, domin ita summa ai ko da hannu ana iya summar da mutun in dai aka daki keyarsa bale da wani makami. Ajiyar zuciya ta sauke gannin ciwon , cikin kwarewa bayan ta hade gashinta ta daure mata shi ta yi maganin ciwon sosai ta saka mata dukan abin bukata sannan ta daure mata shi da farin abin pansama sannan ta juyata ta dora kanta kan matashin kai mai laushin gaske ta shiga duduba jikinta sai dan balshe a cinyarta nanma ta saka mata magani sannan ta nemi jijiyarta ta saka mata karin ruwa dan kadan na dauke zafin ciwon , yana karewa ta cire mata ta yi mata allurar dake iya dawo da ita sannan ta zauna daf da ita tana rike da hannunta mai dauke da allurar nan dan sai ta farka ta ga zata ci gaba da yi mata ne har ta ji sauƙin ciwon ko daga wannan ya wadatar? Bai fi mintina biyar ba Rauda ta ja wani Gwauron numfashi hadi da shedar da ya saka shi dago kansa a hankali ya zuba mata ido Da farko tamkar a lokacin take shirin barin duniyar mutane ta farka, a hankali a hankali ta samu tana jin maganar likitar nan sama sama a kanta tana jimke da hannayenta bibiyu har ta gane a duniya take kuma magana ake yi mata a daf da ita Idannuwanta ta bude da sauri tana waige waige, a birkicen nan da kake farkawa idan ka summa, lokaci daya kuma ta shiga kiran sunnan Abdul Da sauri Salima ta karaso mata shi tana kallonta hawaye na cika mata ido ta saka mata hannunsa cikin nata tana fadin" Gashinan RAUDA ga Abdul din fa" Shima tunda ya ga ta farka ya dora kansa a kirjinta yana fadin" Aunty, auntyna, auntyna" Tunda kunnayenta suka ringa jiyo mata amon muryarsa ta ringa sauke ajiyar zuciya a hankali ta lumshe idannuwanta hawaye na zubowa ta gefe da gefensu dan sarai ta gane a dakin Mah suke, kuma ta gane likita ce ke kanta Baki ya tabe yana dauke kansa a ransa ya ayana' ka ga wani rusheshen d'a ta lalata shi, wannan katon saurayin yana wani runguza mata kai a kirji? Lalle su uwa masu dadi , shi dai soyayarsa da Mah ido ne ta tsolewa mutane ama ai wasu iyayen sun iya shagwaba ya'ya, shi bai isa ya dora kansa a kirjin Mah ba yanzu zata ture tace kai meye haka dilla kauce kar ka fasan kirji!' ( wai Ni ina hadinka da mu ne mai martaba?) Dukkan kular da ta dace likitar nan ta bata sannan ta dawo wajen da yake ta masa bayanin zata dawo dole a gobe dan ta ga yannayin jikinta, idan da sauki shikenan sai ta cire mata allurar karin ruwan in kuwa dole sai an ringa zuwa saka mata magani har ta warware shikenan, abinda dai yake wajibi idan ta warware sai ta je an duba kan a na'ura dan harkar kai ana takatsantsan da ita. Daga nan ta tafi, shi kuwa ya mike da hannunsa ya yiwa Salima alamun ta zo Da sauri ta mike ta je, yana sake duba agogonsa ya ce" Ki zauna da ita har Mah ta dawo, zan je part dina" Da to Salima ta amsa ya fice shi kuwa ya nufi nasa bangaren domin a yau zai yi transfer na kudaden kayan aikin da zasu shigo na ginnin fadar baki dayanta, dan a satin nan za'a fara aiki jajir , domin ya samu da kyar ya lalaba Hajia ta yarda a yi ginnin fadar a mamakeken filin dake jikin tsohon gidan fadar, nan din ya nuna mata yana so a bar shi matsayin gidan dukkan wasu da suka shafi fadar, su waziri da sauransu...... Sunna zaune ne Salima na fama da Abdul kan ya ci kwan da ta soyo masa ama ya kasa cin wani abin kirki dan hanjin cikinsa sun gama kulewa da horon yinwa Mah ta shigo da sauri tana masu salama hankalinta a kan RAUDA dake barci Mai nauyi da kuma Abdul da Salima Jakarta ta ajiye da sauri ta karaso ta zauna tana dubansu zuciyarta na tsintsinkewa tana jin wani abu kamar tsanar matar da bata santa ba, itama bata santa ba na taso mata daga cen cikin zuciyarta Dubanta ta kai kan Salima idannuwanta a kausashe ainun ta ce" Matar nan ce ta yiwa yarinyar nan dukan nan? Lalle yau ba zan iya hakura ba, sai na kuleta!, kennan ita ta dauki kannin na RAUDA? Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, lalle akoy mutanen da basa jin tsoron Allah, na yi ta kiran numbobinku bana samu na yi tunanin baku ji ba ashe ku tashin hankali kuka tarar a cen din? Ba zata ci bulus ba walahi , dan na daina hakura kowani banza yana takani da ahalina dan son zuciya!" Salima dake ta rike hawayenta muryarta a raunane ta ce" Mah, Ni ban taba jin tsoro irin wanda na ji yau ba, ba imani ba tausayi ta ringa maka mata abin nan, ga magangannu tana ci na alwashin itace ajalinta da yaron nan, yaron nan duba ki gani, har yanzu ya kasa zama waje daya du a tsorace yake da kowa, Mah da ace bamu je da direba ba na tabata sai ta idasa nufinta sai ta kashe tan.... ......." Sosai ran Mah ya bace, kuma a yanzu haka in ba dan ta ga cikin aikin da ta baro YUSUF ba walahi da a yau yau sai ya dauki mataki ba sai gobe ba, ama da kyar da rarashi Mah ta dangana har goben, kuma ta amshi kiran da balaraben Rauda ke ta yi a wayar Salima domin ya jima da samun numbar Salimar saboda in yana kiran Rauda wani Sa'in baya samu, nan take shaida masa Raudar ce ba lafiya ama da sauki kuma wayar Tata basu san inda take bane, shima da kyar suka yi salama yana ta aukin fadin dan Allah ta rokar masa Mah ya zo gobe ama Mah fir tace zai zo ama ba gobe ba sai ta ji sauki, da wannan Salima ta je nata dakin ta tarar da yan matan Mah sun baje abinsu sunna sharar barci ta shige bayi dan yin wanka ta bar Mah na ta rarashin Abdul wanda da kyar ya yarda ya yi wanka Mah ta rasa abinda zata bashi ya saka , a dole tufafinsa ya maida ta kwonta da kudirin gobe in sha Allah an je a yi masa siyaya Mah kwana ta yi tana taba goshin RAUDA har kiraye kirayen sallar asubahi suka farkar da ita Kamata Mah ta yi ta shige bayi dan yin wanka, da kyar ta kyaleta ta yi sai da ta rantse mata tana iyawa, da dabara ta yi wankan dan har ga Allah ta daku fa Tana fitowa daure da Tawul Mah ta bata doguwar riga da hijab itama ta shige bayin dan yin wankan domin ita har ta yi sallarta A dadafe ta yi sallar ta gama, tana cire hijabin Mah ta fito, ta karasa wajen wando da rigar da ta dauko mata na barci ta miko mata, kaya ne mararsa nauyi ta umarce ta ta saka harda turare sannan ta kama Abdul dake gyangyandi suka fice dan tunda ta bashi wainar kwon nan jiya a baki ya yarda da ita, suka fita tare Da kallo Rauda ta raka su, a hankali ta sauke ajiyar zuciya ta dauki kayan nan ta saka cikin dabara, sai dai du yadda ta so kar daurin kan nata ya kunce sai da ya kunce, gashin ya bazun mata a jiki A hankali ta duka dan daukar ribom din, kunnayenta basu ji mata bude kofar dakin ba, ta dauko ta mike tana dan lashe lebenta da ya yi fari fat ya bushe sosai ta gyara tsayuwarta cikin dabara ta shiga kokarin kame gashin, ama ta ringa jin juwa na yawo da ita Ta kama abin gadon nan a hankali zata zauna Muryar Mah na yar dariya ta bude kofar ta shigo tana fadin" Baby yau na sha kokowa da Abdul, wai ba zan masa wanka ba, ga yaro to ko YUSUF ba sai da ya kai shekara goma ina darje shi a bahon wanka ba....." Ido ya zarro ya juyo da dubansa ya zubawa Mah, wace ke dariyar abin tana bada labarin da a tunaninsa bai taba hasaso ko Bah ta ba shi ba, sau yau shi Mah ta budi baki tana masa tone tone Shi da kansa bai san ya dan shagwabe fuska yana kallonta hadi da zarro ido ba, ita kuwa da bata san ya shigo dakin ba ta kame bakinta tana furta" Au, ashe bosss din na kusa" RAUDA kuwa ta samu kanta ta zubawa fuskarsa ido, yadda ya yin da yadda Mah ta fada din sai ta ji dariya na son kubce mata duda halin da take ciki, hahahaha wannan garjejen karin shima an taba yi masa wanka? Uwa kennan....., sai dai bata yi dariyar ba ta dai saki murmushin da shi da kansa sai da ya gani har ya dan so shagala da kallonta dan bai taba ganninta a irin yannayin nan ba, yawanci ko tana fada, ko tana rizgar kuka haka dai Mah ta rike caputuno din da ta yiwa RAUDA ama yake son karbewa tana fadin" ka ga ba fa naka bane, yauwa me ya taso ka da sassafe haka kamar ka san a raina ka kwana? Son ko ka kai karar matar da ta sak3ar min yarinya sannan ta sace min yaro ko yanzu na fita na je na kai, dan sai na rufe ta ta je ta hadu da yan daba irinta ko zata yi hankali!" Ido ya sake zubawa Mah, gannin ya ki sakin kofin sai ta sakar masa ta ci gaba da fada sosai kamar shi ya sa aka daki marar kunyar y'arta Yana kallon Mah yana karasawa har bakin gadon da Rauda ta koma ta dan ringesa tana kallon Mah din itama Dubanta ta dago tana kallonsa gannin a nan ne zai zauna, tana yunkurin tashi dan ta bar masa wajen ta ga ya zauna daf da ita tana dan juya cofee din ya kai bakinsa ya dan surba, ga mamakinsu daga ita har Mah sai suka ga ya dan dibo a cokalin nan ya nufi bakin Rauda da shi yana kallon Mah ya ce" Yanzu shikenan dan yau ba ita ta daka ba dan an daketa sai ki rufe wanda ya daketan? Y'ar nan taki har kunne ta cirawa wata a gabana!" Daga Mah din da ta yi mutuwar tsaye gannin da gaske Rauda ce yake son ba caputuno din, da ita RAUDA wace ke kallon wankan tarwadan hannayensa masu fitar da hucin gumi da yar cokalin shan cofee din dake cikin hannun da furucin da ya yi har ta kasa wani motsi , sai baki da ta bude tana dafewa da hannayenta ido a kwalale ta ce" Ni din? Ni kuma?" Fuskarta ya fara tsarewa da kallo, sai kuma ya dauke dubansa ya yi dan murmushi ya ajiye mata cofee dinta a nan ya dawo wajen Mah ya riko hannunta kasa kasa ya ce" wannan in tana son sakani rantse rantse ta kiyayi gaban kakata, Ni dai na fada maku....." Kai jama'a 🤔🤔🤔🙄🙄😒😒😒😒😒😒😒😒😒😒🤒🤒🤒🤒🤒🤒 Azl 28 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo Mah bata san lokacin da murmushi ya kubuce mata ba har gaba daya haƙoranta suka bayyana tana kallonsa, ya kawo hannunsa gefen fuskarta a hankali ya shafa yana kallonta Bai san me yasa ba, duk duniya babu murmushin da yake shigewa zuciyarsa ya dadada masa rai irin na Mahaifiyarsa A tausashe sosai ya furta" smil again fr me Mah" Mah ta sake sakar masa murmushi tana doke hannunsa ta yi gaba tana fadin" Kana nufin matar da ta dakar min yarinya ta daki banza?" Murmushi kawai ya yi, shi fa baya son fitina Allah ma kuwa, bai cika son rigima ba fa, in ana rigima kansa zafi yake dauka, kuma baya son kin gaskiya, in ba neman a yi ba ita kan nawa ta fasa? Dakinsa suka je ya dauko computersa ya ajiye gabanta ta shiga duduba tsarin shagunan da ya mata bayani za'a yi a dora mutane a kai a nan cikin garin Ta dago zata yi adu'ar Allah ya sa a gama lafiya ya sanya alkhairi ta ji yana fadin" To wai Ni yanzu kennan ba Ni daya kika haifa ba?, su wadinncen gasucen har yanzu basu tafi ba, ga wannan ƙatuwar y'ar kin wani dasa mata baby, kuma ɗan natama ke zaki rike?" Mah ta kama haba tana kallonsa ta ce" D'anta?" YUSUF ya dage kafadu yana kallonta Mah ta yi murmushi ta ce" To in banda abinka kai yanzu ai ka girma, Ni kuwa tsohuwa ai sai da mutun a gefena ko? Ko ba zan riki ya'yan yan uwana ba kake so ? Ko kuwa baby ta tsole maka ido ne ban sani ba? Abdul kuwa ai naka ne, dan in fada maka a hannunka yake, duk inda ka je ka je da shi kawai" Shiru ya yi yana zaunawa kusa da tarin kayan da suka sauka yau daga fadar SHAHEED ya kai hannunsa yana dan murza gaban goshinsa, ya ji Mah na fadin" RAUDA kuwa, ka san me yasa nake jinta har cikin raina? Yarinyar nan ta ga rayuwa, koda bata fito ta fadi dala dala ga irin abinda ta gani a rayuwa ba ina ji a jikina ta ga rayuwa, ka san wani lokacin mutun na koyan fada ne idan aka gama matse masa waje fa, son yakan koyo iya masifa ne dan ya kwaci kansa ba dan wani abu ba, ina gannin Rauda ta gama hardace rikicin duniya ta yadda ta koyi kwatar kanta, yau ko ba'a yi maka komai ba idan baka da uwa baka da uba a ringa tayaka da addu'a da rarashi son, ina son yarinyar har raina, ina so na ga rayuwarta ta samu cenji sosai .....ina fatan zaka taya Ni son ta" Kwalayen agogon da yake dubawa yana mamakin SHAHEED ya dage kennan ko? Ya ajiye ya juyo wajen da Mah ke zaune ya dan zuba mata ido, sai kuma ya yi murmushi ya dauke dubansa ya ajiye ya taso ya dawo inda take zaune ya zauna a tausashe ya ce" Ko kare kike kiwo, zan Bashi abinci da wajen kwonciya, zan kula da shi sosai, bale mutun........, koda bayan su kinna son karo wasu ya'yan ki karro, in sha Allah ba zan rasa abin ciyar da su da tufatar da su ba , bale kin ga yannayin ginnin da za'a yi, kowace da wajenta, da dakunan ta da dukkan abin bukatarta, kina da damar sauke wanda kike so ya yi zaman da yake so a wajenki........." Mah ta sauke ajiyar zuciya a tausashe ta furta" Allah ya tsare ka, ya yi maka albarka, Allah ya iya maka dukkan abinda ba zaka iya ba, ya baka mace ta gari .... YUSUF ba zaka taba wulakanta ba, domin ka faranta min , kuma ka faranta wa mahaifinka, laifukan da ka yiwa ubangijinka ka ci gaba da neman yafiyarsa, ka ringa kiyaye daukan alhakin mutun dan uwanka, in sha Allah idan ka kiyaye Wadinnan shikenan ba dai mutun ba sai dai Allah , dan a kulun ina maka fatan alkhairi da samun aljanna a wajen Ubangiji" Idannuwansa ya lumshe yana jin abinda ke ratsa dukan gaban jikinsa, ya kai sau uku yana niyar zuwa ya ajiye rawanin nan kafin ya yarda ya rike, wannan baiwar Allahn kawai idan ya tuna sai ya rike ya ci gaba da rokon Allah alkhairinsa a kan zanen rubutun kundin kadararsa "Malik?" Mah ta fada a tausashe Idannuwansa ya bude yana kallonta hadi da sakar mata murmushi Mah ta ce" Allah bana jin zan iya yafewa matar nan da ta dakar min y'a!" Idannuwansa ya lumshe ya daga sosai daga dan gurfanawar da ya yi a kusan Mah ya zauna sosai sannan ya ce" Nima bana jin zan iya yafe mata" Mah ta sake yi masa kwatankwacin kallon da ta yi masa a dazu da ya so ba RAUDA cofee din nan, da dan gagawa ta ce" Zaka saka a kamata ne ko? Zaka rufe ta ne ko?" Kai ya girgiza yana kallon Mah A tausashe ya ce" Bana tunanin matar nan wuni biyu ko uku a hannun iko zai sa ta saduda da rayuwa..........., ba zan kaita ofishin yan sanda ba, ama kuma ba zan kyaleta ba" Mah ta dan zuba masa ido dan bata so yace zai dauki mataki da hannayensa, bale a yanzu ya dace ire irin abubuwan nan ya hakura da su , dan ana iya yi masa wata fasarar daban, ko magauta su samu hanyar cin masa ta haka" Da kula sosai Mah ta ce" YUSUF, ka ga ina fada maka yanzu banda rigima ko? Shi yasa na dage kan dole a yi maka bayani a kan Shari'a, domin Shari'a abu ce mai girman gaske da abu kankani ke iya kai bawa ga halaka, ka yanke hukunci a kan mai laifi ko Ni ce, ka yiwa marar laifi adalci koda abokin gabarka ne, idan ka san wani abin zaka yi mata da bai dace ba gwara na barta da Allah ka ji?" Murmushi ya yi , ya shiga saukowa Mah akwatunnan dake zube tari tari a saman gadonsa dauke da suturun wajen SHAHEED ya sanar mata sakon wajen SHAHEED ne aka kawo, nan fa Mah ta shiga murnar kayan da mamaki harda sakawa a yi mata kiransa dan ta yi godiya, da wannan ya bada mata zancen suka shige wani daban A lokacin da su Mah suka fice a dakin nan RAUDA ta jima tana kallon kofin cofee din nan ba tare da ta san takamaiman abinda take tunani ba Shigowar Musulima da Salima dauke da kayan karin kumalon da Mah ta saka a yi kowa ya karya , Musulima ta taya Salima daukowa dan kawai ta ga wai menene dalilin da ya sa har YUSUF ya dauko yarinyar nan , suka shigo da salama a bakunnansu, Salima na murmushi tana kallon RAUDA wace ta dago dara daram idannuwanta masu shige da jikakun idannuwa bayan basu da wata jikar hawaye haka yanayinsu yake , gasu a mugun mace , dama matatun idannuwa ne da ita,, kuma ciwon nan ya karra masu dan nauyi sai take kallo kamar na wace ta maku, wani kallo kasa kasa Murmushin ta yi itama tana dauke dubanta daga kallon da Musulima ke yi mata wanda ya zarce misali Da fara'a Salima ta furta" Alhamdulilah, jiki ya yi kyau, yaya jikin ko yar uwa?" RAUDA ta yi murmushi tana amsar plate din da take miko mata ta furta" Alhamdulilah yar uwa, kuma sai kika barni kika gudu kika sa na hanna mamana barci ko?" Salima na yar dariya ta zauna bakin gadon ta mika hannu dan daukan cofee din nan, sai ta ga Rauda ta rigayeta dauka, bayan ta dauka din sai kuma ta dan yi jim kamar zata maido mata , kuma sai ta fasa Salima dai bata san komai ba dan haka ta yi maganarta tana fadin" Ai gwara da kika kwana a gefenta, da ba zata iya barci ba kwana zata yi tana kai kawo dakin cen da nan, ya baki sha cofee din ba? Har ya huce ko" Murmushi RAUDA ta yi ta ciro cokalin dake ciki ta mika mata sannan ta shiga dan sha kadan kadan ta dago idannuwanta, da idannuwanta ta yiwa Musulima alamun yaya dai? Sai a lokacin Musulima ta ankara da abinda yake faruwa, ta dauke fuskarta da sauri tana hade fuskar Tata ta nufi wajen ajiyewa ta ajiye ta juya ba tare da tace da ita yaya jikin ba kamar yadda ta cewa SALIMA, har sai da Salimar ta ankara ama bata ce komai ba, tana ba RAUDA dariyar Abdul , dan yana cen ana auna shi, kuma.da zarar ya karya za'a fita da shi boutique a zabo masa suturun da zai fara amfani da su Kai RAUDAH ta sada, zuciyarta na tsintsinkewa, tana jin wata irin daraja da girman ahalin nan baki daya a zuciyarta A hankali ta dago dubanta tana kallon Salima dake zaune itama ta bararaje tana ta yi mata labari A sanyaye sosai ta furta " Na san a jiya kin cika da tunani da tambayoyi tun bayan tambayar da kika min a lokacin da muka kama hanyar gidanmu, na kasa baki amsa ko?.....kin san me yasa na kasa baki amsa?" Salima ta tsareta da ido tana girgiza kanta a hankali A nutse RAUDA ta ce" Dan na cika da zulumin abinda zaki tarar na rayuwata wanda ban cika budar baki na sanar ba sai idan Allah ya sa ka gani ko wani ya fada maka...., Salima abinda kike gani a jiya kadan ne daga abinda marikiyata tun ina yarinya take iya yi, dan Allah kar ki yi wani tunani a kaina, idan kin ga na yi abinda bai dace ba, na rikice ne dan na rasa tunanina a lokacin da na ga irin abinda ta yiwa Abdul bayan ta sato shi daga wajen da yake da gata ta kawo sun wulakanta, duk irin abinda nake yi dama dan ya tsira ne, dan na san Ni Babu abinda suka iya da Ni, ko ba komai zuwa yanzu na kai wajen da nake iya ja in ja da su baki daya....ama kina kallo suka dauko shi suka wulakanta min shi...." Sai kawai hawaye suka bale mata, a hankali ta dauki tissu tana gogewa tana jin Muryar Salima da ta rike hannayenta tana kallonta tana fadin" Dan Allah ki yi hakuri, ki yi hakuri da abinda ta makiy tabas ta kasance mutun mai son kanta da kin jin tsoron Allah, kalaman ta kuwa sun yi tsaurin da ban san a wani bigiri zan ajiye su ba, tsabar jahilci ne ya sa ko kuwa rashin imani? Abinda na sani shine a yanzu daga ke har Abdul kun fi karfin ganninta bale har ta kai hannu jikin ku, ita kuwa ta yi jiran sakayar Ubangiji a kwana kusa !" Ajiyar zuciya RAUDA ke saukewa a nutse ta furta" bi'izinillah kam, babu ita babu kuma cutar min da Abdul, dan kuwa idan na maida shi wajen inna sai na sa hukuma ta shiga tsakaninta da shi!" "Gidan inna?, Wacece inna?" Salima ta fada tana kallon RAUDA RAUDA ta ce" Kakarsa ce" Salima ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Aya, bawan Allah, mahaifinsa baya kasar ko? Ashe kakarsa da rai? Masha ALLAH " RAUDA ta gyada kanta a hankali tana dan murza yan yatsunta ta ce" Da ranta, mahaifiyarsa ma tana da rai, mahaifinsa kuwa shine uncle dina wanda ya rike Ni" Da sauri Salima ta kalli RAUDA, sosai ta so yin magana ama ta kasa ta hanna kanta, ama a zuciyarta mamaki fal ya cika mata zuciya, wai dama Abdul ba d'an RAUDA bane?, ikon Allah ama sun shaku da junna kamar yaronta, kofa yake yadda take nunawa ne kowa zai yi tunanin ɗan nata ne, ama RAUDA akoy karfin hali da zuciyar tausayi, ta yiwu abinda ta gani saboda yaron ba kadan bane a rayuwa, sai ta ji ta sake shiga ranta da tausayinta sosai Tana murmushi tana kallonta ta ce" Ki fa ci, Mah tace ki ci sosai, tana dakin yaya MALIK ne, kin san da wahala yanzu kuma Mah ta bada Abdul?, bale idan ya nuna ba zai rabu da ke ba, ita kuma fa ta yi y'a, babu mai rabata da y'arta sai mutuwa da aure" RAUDA ta yi murmushi, a ranta tana tunanin abin ai sai ya yi yawa, ita da kanta da ace namiji ne ya kai shekarunta da tabas ta wuce riko, bale kuma ta karra kawo wani? A'a in sha Allah da zarar ta warware zata je banki ta kwashe duka kaf kudadenta ta gyara gidan inna sosai sannan ta siya masu kayan abinci sosai, kuma ta saka shi makarantar kudi ta daukar masa Aminu mai adaidaita ya ringa kaishi yana dawo da shi, kuma ta saka hukuma ta shiga tsakaninsa da su Mama, kafin ta koma ta rama abinda suka yi mata, domin ta kudurci aniyar ita da su za'a dora ne da kare jinni , biri jinni! Ta dan taba abincin, barci ya ringa sandarta, ama bata kwonta ba har sai da likitar ta zo ta karra saka mata karin ruwan nan , ta kuma bata magunguna sannan ta tafi, tana tafiya da yan mintuna barci ya yi awon gana da ita, hakan ya sa Salima ta daidaita mata sanyin acn ta kashe mata fitila ta kwashe kayan abincin ta rufo mata dakin ta tafi wajen sauran yan matan dan su fitar da kayan girki, domin kwarai akoy yan aiki ama tunda iyayensu suka nade hannaye suke harkokin gabansu sai Mah ta nuna masu ita fa ba zai taba yiwuwa tanada yan mata kamar su wasu su ringa masu girki ba, a dole sauran da basa so suke haduwa da wa'inda hakan ya masu daidai dan dama sunna son girki suke yi tare Kusan wuni RAUDA ta yi tana barci, ko Abdul dabara aka yi ta masa, karshe aka kunna masa tv sai kawai ya yi zaune sallah kawai ke tashinsa, shima sai Mah tace idan bai tashi ya yi sallah ba zata dauke TV din abinka da yaro tsaf ya yi wuri ya ajiye RAUDA yake sha'anin sa, cikinsa ba yunwa, jikinsa da sababin kaya, ai sai farin ciki Sai da yama Mah ta tashi RAUDA da kyar dan abin maganin nan bai barta ba ta saka ta yi wanka ta cenza tufafinta zuwa doguwar riga marar nauyi ta dauki mayafinta ta bude shi ta yafa a kanta sannan ta fita wajen su Salima tana takawa a hankali ko zata ji dadin jikinta sosai dan ta jima a waje guda a kwonce tun jiyan nan, gashi bata saba ba Sunna nan sunna yar fira a baban falon gidan, har magariba ta kusa shigowa Mah ta fito da sauri, ta dube su ta ce" Yan Matana zamu je asibiti an ce abanku ya farka wai, Please ku kula da kanku sai na dawo, baby ki sha maganinki fa, sai na zo" Ko iya tsayawa ta ji adu'ar da suke yi bata yi ba ta fice, bayanta su Hajia suka fito summa ko ku ci kanku basu ce masu ba suka ficewarsu, hakan ya sa Salima dake ta murna ta nufi mahaifiyar dawowa jiki a sanyaye ta zauna hadi da dan dafe habarta da yatsarta manuniya tana kallon RAUDA dake mata alamun ta ware ba komai Murmushi ta yi mata ta sada kanta bata iya sakin jikin nata ba, karshe kiraye kirayen sallah ya saka su mikewa kowace ta nufi hanyar da zata daura alwallah dan yin Sallah, RAUDA kam da Abdul ta tafi dakin Salima dan ta fi sakewa a cen, bale yanzu da Mah ta fita Tun sunna saka ran dawowar Mah har suka fara cire rai, domin su Hajia tuni suka dawo kuma basu sanarwa kowa yadda jikin marar lafiyan yake ba, hakan ya sa suke cikin damuwa dan sunna son jin yaya jikinsa sosai, bale ita RAUDA ta fi damuwa bata san dalili ba, ko dan ta ga a duniya wannan matar dake nuna mata soyaya tana matukar son wannan bawan Allahn ne? Ita dai tana masa fatan samun lafiya har cikin zuciyarta Gannin karfe tara tana neman yi ta karɓe wayar Salima da Abdul ke buga game din da ko iyawa bai yi ba ta ce maza ya mike ta masa wanka ya cenza kayansa Kayan da ta dauko ya kalla, riga da wando ne na barci da pant, pant dai pant na mata aka hado a cikin kayan nasa na barci, ita kuwa bata taɓa Sannin wai ba wandon maza bane dan haka tace ya shige su je Da yannayinsa ya shiga make kafada yana fadin" Aunty, to sai nawa zan yi wankan? Ni dai a'a, mura zata kamani, a'a aunty, kuma ba zan cire kayan nan ba kar aje wani ya dauke min, ina son su" Da yannayin rarashi tana rike mayafin rigar jikinta ta ce" Abdul dina, mura ba zata kamaka ba, ka ga a nan sau uku ake yin wanka fa, kuma kayanka babu wanda zai dauke, mu je dan albarka na maka wankan ka ji?" Shi kam sai ya ga abin wani iri, kuma yau auntynsa ce zata masa wanka bayan a da ba ita ke yi masa ba? Abinka da yaro sai kawai ya juya ya diba a guje yana fadin shi dai a'a ba zata yi masa wanka ba, ba zai cenza kayansa ba! Ido ta zarro, gannin dare ne fa, kuma ga gida na yan gayu ba hayaniya suka cika so ba, gashi a gidan ta jima da gane ba kowa ke ra'ayinta ba,sai ta dauki sauri tana fadin" Azl 29 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo Da sauri RAUDA ta biyo bayansa tana fadin" Kai, Abdul, zo nan, baka gannin dare ne ba kyau gudu da dare? Zo nan ina wasa da kai ne?" Tana fada tana karasowa falo ne, hadi da ja ta tsaya ta rike tsatso tana hada gabas da yama irin bata son wasan nan dan ta kula idan ta ce zata tsaya yi masa dariya yana iya janyo mata magana ne Kai ya dago daga danna wayar da yake yi ya zuba mata ido, irin tsayuwar da ta yi tana tafka harara ta saka shi juyawa dan gannin abinda take yiwa hararar , gannin Abdul na nufarta yana shashekar kuka alamun yana iya fashewa da kuka ya saka shi tabe baki hadi da girgiza kai a ransa ya ayana' dama kema ba fita rainon kika yi ba, kuma sai Allah ba baki wani rainon, bawan Allah, Allah ya sa kar ta rikita yaron nan' " Kai, yaushe na fara maka magana kana raina Ni? Nace mu je na maka wanka ka cenza kaya ne zaka wani fita a guje? Ya maka kyau wuce mu tafi!" Ta fada tana zazaro masa ido da nuna masa hanya hadi da fitar da pant din dake hannunta dan da shi a hannunta take nunawa tana yin fadan Idannuwansa ya kankance yana kallon abin da dukkanin son ya gane abinda ke hannun nata, ita kuma tunda ta fito Allah bai kai hankalinta kan babar kujerar falon na, ko dan ba abinda ya fitar da ita ba kennan, duk kuwa da irin yadda hancinta ke jiyo mata kanshin turaransa wanda zuwa yanzu ta gama gane nasa ne, bata saka cewa shi din ne a wajen ba, dan ta gama hardace turaransa koda baya nan kana iya jiyo kanshin a waje, tsabar nacin kanshin turaran ya sa duk inda ya shiga yakan bar kanshin ne na dan lokaci bale wajen da yake rayuwa "Wandon waye a hannunki kuma?" Ya fada yana asalin ajiye wayar hadi da zuba mata ido Har ga Allah bata taɓa kawowa zata ji muryarsa a kusa kusa ba, hakan ya sa ta daka tsalle hadi da yin dan ihu tana dafe kirjinta hadi da kallon inda yake zaune " Haba bawan Allah sai ka saka na kamu da hawan jinni mana!" RAUDA ta fada, kanta tsaye, ba tare da ta ankara da wa take maganar ba, har sai da ta dasa aya sannan ta sake kallonsa a sace, a hankali ta sunne kwayar idannuwanta kasa kasa ta furta" Sorry Please" sannan ta juya da dan sauri da nufin tafiya "ZO NAN" ya samu harufan bakinsa da fitarwa a wannan yannayin Dakatawa ta yi da tafiyar da take yi, a hankali ta juyo tana kallon Abdul da mamakin gannin ya rigayeta zuwa inda aka ce mata zo nan kamar wani babanta A hankali ta karasa ta zauna saman daya daga cikin kujerun ta sada kanta tana sauke ajiyar zuciya dan bata san irin fadan da zai yi mata ba kuma Kai ya girgiza yana kallonta ya ce" Ke Ni fa na girme ki, yaya zaki zauna saman kujera bayan ina sama? Kuma ama bakya tsoron Hajia ko?, baki san ta hanna ire irin abubuwan nan ba?" Dagowa ta yi a sanyaye ta zuba masa ido, ta ga ita din yake kallo , kuma amsarta yake jira, dan haka a hankali ta furta" Ka yi hakuri" "Ki fadi abinda kike tunani sak ya fi" ya fada yana dauke kansa bayan ya sakar mata hararar Kai ta sake sokewa, a ranta ta ayana' ikon Allah ' A bayane kuwa ta furta" Dan Allah ka yi hakuri" , ama kuma ta ki saukowa daga saman kujerar , kai ita har ga Allah bata ga me yasa zai ce wai ta sauka na, toh haka kawai dan ya ga Mah bata nan ko? Ido ya sake zuba mata, tana dago kai ya dauke dubansa ya mayar kan Abdul dake mota mota a falon yana kallonsa, kasa kasa ya ce" kin sha maganinki?" RAUDA ta sake zubawa fuskarsa ido, ya Salam ta ringa ambata a cikin zuciyarta saboda bugawar da kirjinta ke yi "Eh na sha" ta fada itama a kasa kasan "Kina iya tafiya" ya fada yana juyowa ya saka idannuwansa cikin nata Gabanta ya sake yanke wa ya fadi, da sauri ta mike tana rintse idannuwanta dan jin wani irin gumi ma son tsatsafo mata "Ji mana" ya fada muryarsa a mugun kasalance A hankali ta juyo ta zuba masa idon itama, shi kuwa bai risinar da nasa kallon ba yana kallonta tsai cikin ido da kuma bandejin dake goshinta wanda ya mata kamar an yi mata kwaliya ne, kasa kasa ya ce" Mah ta ce, ki kula da kanki" RAUDA ta lumshe idannuwanta hadi da gyada kanta "RAUDAH " ya sake furtawa ba dan ya san me zai kuma ce mata ba, RAUDA ta bude idannuwanta da suka cika da kwallar da bata san ko ta mecece ba YUSUF ya dauke nasa idannuwan da suka yi Jajajir bai kuma ce mata komai ba, a ƙalla ta dauki minti biyu tana jiran amsarsa har ta sake yin baban motsin da zai sanar masa tana nan fa, dan sai ta yi tunanin ko ji yake ta tafi? Ba tare da ya sake kallonta ba, a hankali ya furta" good night " Sake duban fuskarsa ta yi, ta samu kanta da binsa da kallo tun daga kansa har zuwa kaffafuwansa dake cikin fara kar din Safa Bata san dalili ba, kallon da ta masa na farko ta ji bai ishe ta ba har sai da ta maimaita masa ya kai sau uku, ko wani abu take son ganewa a tatare da shi? Ita dai ta san ta masa kallon da ya wuce Shari'a, wanda ba zata tuna namijin da ta taba yiwa kallon nan ko dan ta gane shin namijin da zai bata kudi ne bata cika yin irin kallon nan ba, bale wannan da ko kusa bata kawo irin abin nan a ranta ba A hankali ta juya tana jimke hannun Abdul da ya fara gyangyandi ta nufi dakin Salima da shi Sunna juyawa ya dago kansa ya rakata da kallo har sai da ta bacewa ganninsa sannan ya girgiza kai ya yi dan murmushi ya sake karanta sakon Taj na abinda ya saka shi jiya da kuma sanar masa da ya yi jikin Umar da sauki sosai dan ya fara fira da tambayar wanda ya kawo shi asibitin da tambayar idan da hali a kai shi ya ga danginsa Msg ya shiga masa typing da turanci yana fadin" Ka ce ya kwontar da hankalinsa ya samu sauki sosai, ka ce masa RAUDA na gaishe shi zata zo su tafi, ina so a gobe gobe ka je gidansa ka min bincike a kan matarsa, kowani bawa baya rasa abinda ke iya dakatar da duk wani farin ciki nasa na duniya, ka gano minenene" Daga nan ya kashe wayar ya ajiye ta ya lumshe idannuwansa yana jin yadda kansa ke masa nauyi A dazu mahaifinsa ya farka, har ya ga matansa, kuma cikin ikon Allah sun samu bai daga hankalinsa ba, domin a lokacin da ya tambayi ya jima a kwonce? Aka shaida masa sai ya kama hannun Mah ya jimke kawai yake sauke ajiyar zuciya, a nan ne ita kuma ta zauna daf da shi, ta rike hannayensa cikin irin Tata baiwar, wace Allah ya bata damar tankwasa tashin hankalinsa da bacin ransa ta ringa yi masa bayanan yadda zai gane, har ta kai aya yana kallonta da yannayinta, a nan ne ya yi mata tambayar wa aka naɗa sarauta? Zuciyarsa na tsintsinkewa, dan ba zai taba son a nada cousin dinsu ba, domin kowa ya san me aka naɗa, kuma ba zai so ace sarauta ta shiga hannun Nana ba, dan ta fara bashi tsoro, kuma ya san YUSUF ba zai taba amincewa da sarauta ba, ba zai amince ba, bayan a dukkan tunaninsa da hasashensa bai ga wanda ya dace da ita ba Shine Mah ta shaida masa wanda ya hau, abinda ya saka shi zarro ido da mamaki, bashi da wani karfi ko kuzarin kirki a jikinsa ama sai da ya jimke hannunta da dan karfin da yake ji a jikinsa ya ringa neman a kirawo masa YUSUF din, a lokacin kuwa YUSUF din na cikin baban daki sunna ta karatun abinda ya shafi sarauta da asalin nauyin da yake wuyansa, a dole aka bashi hakurin cewar zai zo, nan ne doctern sa ya nuna shi kam idan da hali a tsagaita surutun dan kar ya hadu da ciwon kai da na idannu a bar shi ya huta kar a cika shi da surutu, ya farka kwarai, ya yi kyakkyawar farkawa, ama ba'a san me yake boye ba, sai an bi shi a hankali, shine su Hajia suka ce Mah ta tashi su juya ta nuna ita kam babu inda zata je kuma sai YUSUF ya zo sa koma tare, sai gashi YUSUF din bai gama da wuri ba, sai waya suka yi likitan ya nuna masa ya zauna gobe ya zo, sannan Mah ta nuna masa zata kwana a nan, dan har zuwa lokacin ya dan koma barci ne ya farka, kuma idan ya farka din yakan kama hannunta ne ya sakar mata murmushi, ga dukkan alamu haka din yake so. Shine fa ya zo ya zauna a falo, kowa ya bashi waje yake zaune yana duba wayarsa yana ta amsawa mutanen da bai samu ya amsawa ba, abubuwan ne sun masa yawa, har su RAUDA suka fito suka dakatar da komai ya shiga sabgar da ba tasa ba, sabgar wa'inda a ganninsa bai dace ya shiga ba, ya kananage har ya dage kan sai ya ji wani abu daga gare ta da ya danganci amon murya, ko yannayin nan nata na fada, sai ta karra neman saka shi a tunani har ya girgiza kai ya yi murmushi yana ayana' me yasa komai nata yake daban?' Sai kuma ya ture zancen ya mike ya je da kansa ya kashe fitilu ya rufe babar kofar sannan ya nufi dakinsa, kansa ba rawani, a hannunsa ya rungume rawanin, shi yana tunanin koda ya yi rowar fuskarsa kamar yadda akace dole sai ya yi, banda cikin gida, baya tunanin zai iya yawo a cikin falon su,da dakinsa zuwa na Mah da rawani sai kace mai gyambo Daren nan, ya kusan rabawa zukata uku cikin kai da kawon tunanin sarkakiya mai wuyar fassara, domin a irin lokacin da wasu zukatan ke son ture abinda ke saka su murmushi, a irin lokacin ne zuciya daya jal mai cike da kauna da tarin bege ke kwonce a baban Center na kula da lafiyar zuciya ta garin ana bata kula daidai da rikicewar ta da jajircewa da ta yi kan lalle sai an fasa an cenzata domin bata san Yaren ta yi hakuri za warke ba, a lokacin ne mai dauke da zuciyar ya kafawa waje daya ido yana auna shekarunsa a mizani, inda ya tabatarwa da kansa cewar koda babu lalura irin ta jinyar zuciya a yanzu da ya haura hamsin idan ya hadu da ciwon ajali ba abin a firgita bane, san mutuwa ta dauki jariri bale shi, sai dai abu daya da zuciyarsa ke masa naci itace! Yana son ta! Yana matukar son ta! Ta ina zai fara misalta rayuwa babu ita? Baya misaltawa kansa bale har zuciyar ta buga tashi daya Ya fi sakawa ransa zata dube shi fa, jinkirin nan da bata waigo ba da gasken gaske lokaci ne A yanzu da ta sanar masa ance ya zo, sai ya ji salama, sai dai a jiya zuwa yau da ya ji salamar abin na neman kubce masa dan jin bata da lafiya kuma an ki a bashi damar ya zo ya ganta..... Shin marikanta basu san ba kowa yake da lokacin nan a duniyar ba? Kwarai Allah kadai ya san ranar rasuwar kowani bawa, ama a yadda alamu suka nuna koda baya so dole zai fara hada kayansa Ba zai tashi ya yi ta tafiye tafiye dan neman magani ba, a haka har ya cinye lokacin ba tare da ya yi mafi mahimmanci a gare shi ba Ba kuma zai yarda ya yi ta zuba dukiya a kan abinda cikin dashi dari daya ake yiwa hasashen tashi ba, kai koda zai je ya dasa ya fi so idan ya malaketa ta yi jinyar sa..... Idannuwansa da suka yi laushi ya daga a hankali yana tuna irin firar da suka yi da lauyansa a kan abinda ya shafi dukiyarsa, shi kam bayan na taimakon marayu, gine ginen gidajen marayu, su rijiya da masallatai a wajen da suka dace waye zai barawa dukiyarsa bayan ita?, to ai koda da ransa ita din ce bale idan ya tuna ta yiwu ya rigayeta barin duniyar? Allah shi ke dasa so a cikin zuciyar wanda ya so kuma abin al'ajabin kowa yana so baba da yaro Wayarsa ya laluba da hannunsa na dama da kyar ya dauko ya shiga buga numbar Salima da adu'ar Allah ya sa ta dauka, dan dare ya yi ta yiwu ta yi barci A irin lokacin ne RAUDA take kallo a wayar ta Salima dan rashin abin yi, gashi ta sha barci ya ki daukanta ga tunanin da ta dasawa gayar sodi dan bata ga abinda ya kai kare layin ragunnan laya ba! Sunnan take kallo, haka kawai taji kamar hankalinta zai tashi duba da lokacin karfe biyu ya gota na dare Da dan gagawa ta daga kiran, muryarta cen kasa ta yi salama lokaci daya tana fadin" Abdallah, lafiya baka yi barci ba har irin wannan lokacin?" Ajiyar zuciya ya sauke a hankali da yannayin jinya ya ce " yaya zan iya yin barci Bayan zuciyata na neman fashewa dan ban kaita ta ganki ba?, Please ki bar dattijon saurayinki ya ganki noory" "Mah ne tace sai na warke" Rauda ta fada a hankali Ya buda idannuwansa shi dinma a hankali ya furta" idan na mutu fa kafin lokacin?" Da sauri ta bude idannuwanta ta ce" Wai kana ina ne?, baka da lafiya ne?" Da yannayin muryarsa mai rauni da abin ciwo ya furta" Alhamdulilah" Idannuwanta ta lumshe, dan sarai ta san me amsar ke nufi, idan bashi da lafiya bai cika yi mata dala dala ba, yakan bi ta da alhamdulilah, tun bata gane ba har ta gane A tausashe sosai ta ce" Ka kwonta da hankalinka,Abdallah tunda aka baka damar zuwa, na tabata aurenmu ba zai dauki lokaci mai tsayi ba, kuma kar ka damu in sha Allah gobe idan Mah ta dawo daga wajen Bah zan sanar mata, na san zata ce ka zo ne, zamu hadu gobe in sha Allah ka ji?" Murmushi ya saki, harda sauke ajiyar zuciya sannan ya ci gaba da hirantarta , ita kuma ta bashi dukkan hankalinta har shi da kansa ya yi mata sai da safe sannan ya kashe kiran ta kwonta................ 🤔🤔🤔🤔 Su waye yan team BALARABE SAK????????? KU ZO MU KAFTA Azl 30 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo Washe gari da safe Mah ta dawo, kana gannin fara'ar dake fuskarta ka san nutsuwarta ta dawo jikinta, sai da YUSUF ya isa asibitin aka dawo da ita Tana zuwa jikin y'arta ta fara dubawa sannan ta wuce dakinta ta shige wanka Sai da ta kimtsa jikinta sosai tana shirin fita dan neman abin kari RAUDA ta buga dakin ta shigo bayan ta bata dama ta ajiye kular dake hannunta da plate da cokali tana kallon Mah da murmushi itama a fuskarta ta furta" Barka da warhaka Mah, yaya jikin Bah?" Mah ta saki murmushi ta karaso inda take tsaye ta kama hannunta suka zauna tana mata alamun ta zuba mata abincin ta ce" Bah din ku, yana lafiya alhamdulilah, ya yi hakuri sosai ya karbi kadararsa, ko yanzu sunna fira da YUSUF na baro su" A lokacin da Mah ta furta sunnan YUSUF sai da RAUDA ta ji gabanta ya fadi, ama ta ture ta sakawa Mah cokalin tana murmushi ta ce" Allah ya karra masa lafiya da dangana, ya jikan sarki" Amsawa Mah take yi, da kula, da wani yannayi na gaske wanda take ji Yawancin lokuta idan tana fira da YUSUF, dan haka ta dubi RAUDA bata son firar tasu ta katse ta ce" Ina Abdul? Ban ganshi ba tun dazu" RAUDA ta yi murmushi ta ce" Salima ta yi bako shine ta ja shi dan ya rakata" Mah ta yi murmushin itama tana kallon RAUDA ta ce" ki dan bani labarin soyayarku da Balarabe mana? Daughter kina son shi?" RAUDA ta yi wani kiskirim dan har ga Allah tana ji a ranta da wahala ta iya wannan firar da Mah, kai, yaya zata iya yin irin maganar nan da Mah kuma?, maimakun ta bada amsa sai ta sunne kanta cike da jin kunya Mah ta yi murmushi a tausashe ta ce" kar ki ringa sako kunya a zamantakewana da ke, Ni uwa nake a wajenki, kar ki yi tunanin zan dauke ki na ba wani aurenki ba tare da na tabatar da kina son sa ko akasin haka ba, dan Ni na san cewa auren soyayya duk rintsi ya fi auren da ba na soyaya ba dadi, domin kin ga shi zaman aure fa ba wai irin na kunna soyaya bane, zaman aure ibada ne RAUDA, duk macen dake zaune a gidanta komai kudin mijinta ko takaicinsa, komai addininsa da nata akoy ranakun da ake iya wayar gari da tashin hankali, rigingimu kala kala akoy su a cikin gidan aure, kuma da ba kiyaya ta sa ake haduwa da ire irin hakan ba, zama waje daya ne da yau da gobe wace ta fi karfin wasa, baby sai ki ga idan irin an hada auren nan ne motsi kadan ana kai kara ana yaji, rashin hakuri da junna zai yi mugun tasiri wajen gaza jin dadin zaman, shi namijin da halaya ta yau da gobe da kuma gannin hada shi aka yi, itama macen sai ta ga ai ba zata iya wani hakuri ba gaskiya, shine zaki ga wani gidan ko an hakura ana zaunen kulun cikin rigima ake, wanin kuwa rabuwa ake yi, wanin kuwa an hada din ama kuma idan soyaya ta shiga da yarda da junna zaki ga sun zauna kalau, duka aure dai ba kamar na soyaya, dan in yana son ki, zai ringa daga maki kafa wajen wasu abubuwan, ba fa ana nufin zaku zauna kulun ku cikin dariya ba, No, zai zamo ne koda halin a yi rigimar ta kama zai yi mai sauki, kuma idan ya yi fushi da ke zai sassauta maki da wuri ya yafe maki, haka kema zaki kasance mai yi masa uzuri, idan ya baki zaki yi da abinda ya baki ne, in babu zaki kasance mai talafawa ne da dukkan dabarar da Allah ya hore maki, in fushi ya haɗa ku da junna zaki kasance mai neman hanyar da zaku shirya kanku cikin ruwan sanyi, tsakaninku dai ba wai babu sama da kasa bane na rigima, akoy sosai, sai dai babu wanda zai ji tsakaninku, shi yasa nace Ni da ina da dama da na ringa kawo shawarar a ringa aurawa kowa wanda yake so" Mah ta ajiye maganar a nutse da kula tana kallon yadda RAUDA ke dan murmushi RAUDA kuwa, sauraron Mah take yi tun daga farko har inda ta dasa aya A zuciyarta kuwa tana ayana' Mah kennan, idan haka za'a bi lalle za'a samu saukin wasu abubuwan, ama kuma da yawa ba zasu yi auren ba, bayan wannan Mah duka kaf Yaren soyaya da sauransu na yar gata ne ba wai Ni RAUDA ba, yaushe zan tsaya batawa kaina lokaci da maganar soyaya? Zan iya yin aure idan ba hali na kara gaba, to rayuwar tawa dukantama ai ta in da hali ko ba hali ce, Allah dai ya sa mu dace" A fili kuwa a tausashe sosai RAUDA ta sada kanta tana fadin" Hakane Mah, yanzun ma ABDALLAH ne yace na roka masa alfarma yau ya zo ya gaishe ki, sannan ya ga jikin nawa wai" Ta karashe maganar tana ji kamar wace ta yi wani laifi a harshenta, da shayin furucin bakinta kamar wace ta fadi abin a tuhumeta?, sai hakan ya zame mata sabo, kai, ikon Allah, ita RAUDA? To ko tsakiyar dare ta so yin zance ai yinsa take yi hankali kwonce bale yanzu? Allah kennan Mah ta yi murmushi , sosai ta so sai ta gama jansa a kasa kafin ya zo gidan nan, sai dai wani tunani da ta yi ya kashe mata gaban jiki har ya saka ta ba Rauda damar ta sanar masa ya zo bayan sallar Isha, dan ba zata so abinda ya sameta ya samu koda makiyinta ba, domin ba zata taba mantawa ba, mafarin abinda ya sa suka fara haduwa da mahaifin YUSUF a anguwa su yi fira dan an hanna masa damar zuwa zance gidansu, ance wai ba yanzu ba sai ta gama digiri dinta, duk yadda ta so su bata dama suka kiya, Ajiyar zuciya ta sauke bayan RAUDA ta fita a hankali ta furta" BI IZINILLAH, DA ADDU'A, DA KIYAYE DOKOKIN ALLAH, ABINDA YA FARU DA NI BA ZAI FARU A CIKIN AHALINA BA, CIKI KUWA HARDA KE RAUDANA, ZAN SANARWA YUSUF IDAN YA SHIGO, ZAMU BASHI DAMA YA ZO SAU DAYA YA GAISHE MU SU DAN ZANTA KAFIN MU BASHI DAMA TA BIYU WACE ZATA BAMU DAMAR SANNIN WAYE SHI, SAI AURE......ALLAH YA TABATAR MANA DA ALKHAIRI" RAUDA na komawa ta dauki wayar Salima ta kirayi numbar Abdallah Ta yi ta ringing bai daga ba dan haka ta Bara masa sako, dan tana kyautata zaton yana barci ko yana wani abin da ya sa wayarsa bata kusa da shi Karatun novel ta shiga yi , wanda ya kusan cinye mata lokacin dan sam bata jin barci, kuma nata jin ciwon kan, haka kuma ba barinta shiga kicin Mah zata yi ba, tunda su Abdul suka dawo da Salima ta bashi littafinsa na karatun addinin Musulunci suka fice sai ta nutsu a karatun littafi har sai da kiraye kirayen sallah suka sakata ajiyewa ta mike tana mamakin gudun lokacin ta nufi bayi Bayan sun gama cin abinci Mah ta kiraye su gaba dayansu ta sanar masu tana so su shige kicin uku, sauran biyun kuwa su shiga gyaran falo baba da karami saboda MALIK zai yi baki , kuma RAUDA na da bako Tunda Mah ta fadi RAUDA zata yi bako Musulima ta samu salama a zuciyarta, har ya zamto ta saki ranta da jikinta kamar sauran suka shiga hada hada, dan ta riga ta sani da ace akoy wani abin da take hasashe da wane mutun in ji mutuwa, bako ko na jinni ne ai sai an tantance in dai wando yake sakawa ba sket ba , saima ta samu kanta da yaba girkin da suke yi harda yannayin halittar Raudar a ranta, dan wani sahihin salihin kyau da Allah ya zuba mata mai sakawa a yaba mata koda ba'a so, domin tun daga kalar fatar jikinta har kirarta ta keru iya keruwa yan falo kuwa sunna cen sunna mopping da cenza su labulaye da bade gidan da turarukan wuta da na ruwa, ya zamo tun kusan magariba idan ka tunkaro falon sai dai kanshi ya yi maka maraba Abinci kuwa manya manyan kuloli na alfarma ne ke jere saman table , kallonsu kadai zai iya baka sha'awar cin su Ana kiraye kirayen sallar magaribar Mah ta umarce su kan su je su yi wanka su yi sallah su huta Har sun juya zasu kama hanya Mah ta yi kiran RAUDA ta sanar mata saman gadon ta akoy abaya ta shirya da ita saboda bakonta Cike da jin kunya ta wuce dakin na Mah ta dauko Abayar sannan ta debo turaran wuta saboda sabo da ta yi da anfani da shi ko a gidan uncle dinta, ta dawo ta shige dakin SALIMA ta zauna sunna fira da Salimar saboda yan matan da suka rigaye su kama bayin, ta karshe na fitowa Salima tace RAUDA ta shiga, itama tace a'a ta je ta fito sai ta shiga Yau babu harare hararen nan nasu a tsakaninsu da ita, dama su suke yin abinsu ita sai dai ta kalle su ta yi murmushi bata taɓa kula haukansu ba, dan kuwa basa gabanta gaskiya kuma ko me suke takama da shi su suka gano ba ita ba Abayar ta dora a saman kujera mai raga raga ta saka mata turaran wutar nan sannan ta dauko wandon ta irin na cikin nan ta dora da bra kafin ta shige wankan bayan SALIMA ta fito Bata wani jima sosai a ciki ba ta fito ta shiga gabatar da sallarta, tana gamawa ta dora ta Isha domin an yi tuni Cikin nutsuwa ta shiga shirya wa bayan ta sauko kayan gyaran fuskar SALIMA Tana tsakar caje girarta SALIMA ta shigo, itama ta dandatsa lesh mai shegen kyau ta saka hijab a sama tana ta hidima da bakin da suka zo bayan an gama sallar Isha, Wayar dake hannunta ta miko mata tana fadin" Kin san kuwa da ABDALLAH ya jima a falo karami? Har sun gaisa da Mah sun jima sunna fira , kiri kiri Mah tace a barshi ya yi jira wai, Ni dai na sanar maki dan Allah ki yi ki gama a zaune kike yanzu fisabililahi?" Da mamaki RAUDA ta kalli agogon bangon dakin , sai ta ga ashe karfe tara ke neman yi, ikon Allah lokaci yana gudu yanzu, ama bayan ta gama sallah sai da ta yi su turaran wuta a jikinta da sauransu sannan ta zauna ta shiga tsara fuskarta kamar yadda ta saba, wato boyayiyar kwaliyar dake mahaukacin fito da fuskarta da baban sirrin dake saka maza haukacewa a kanta, domin ko kalar saka kwalin da take yi yana matukar tasiri wajen ladaftar da kallon cikin ido ta ce" kina nufin cikin aka shigo da shi?" SALIMA ta zauna tana kallon yadda ta yiwa girarta sai mamaki ya kamata ta ce" dole zai shigo ciki kar ki manta mutumen da ake saka ran zamowa mijinki ne, wai dama kin iya mak'up?" RAUDA da ta mike tana kallon call din na sake shigowa nasa ta karasa wajen tufafinta ta sauko su tana fadin" Mak'up sai an iya aunty Salima?, ka iya daidaita fuskarka ya wadatar ban fa shafa hoda ba" Da sauri SALIMA ta mike jin ana kiranta za fice tana fadin" zamu zauna ne my kawa, Please ki yi ki fito na kai masa abinci ya ki ci" Murmushi RAUDA ta yi ta shiga kimtsawa Bayan ta saka Abayar ne ta warware gashin kanta ta caje shi bayanta, bata saka masa ribom na ta dauki dan kwalin Abayar ta bude shi ta dan ninka gabansa kadan ta daidaita shi sosai ta caka dauri irin na zahra Buhari ta ya fito sosai ya hau saman suturarta dan sai ta fito dasss da ita tamkar ka sace ta ka gudu Turaran ruwa, irin mai kaurin nan, mai sansanyan kanshi ma Madina za bude ta shafa a jikinta sosai dan shi ba'a shafawa tufafi dan yana iya yin dan maski maski, shi ta shafa a matsayin mai domin bata cika son shafa mai ba,sannan ta dauko wayar wajen SALIMA ta nufi wajen kujerun da yan matan nan suke ta saka takalminta plate ta juya ta fice a dakin na tare da tace masu komai ba, ta bar idannuwansu da rakata da kallo har sai da suka kula da sun bita da kallo ne su dukansu sannan kowace ta dauke kanta A nutse take takawa, kwarai kunnayenta na jiyo mata firar maza sama sama haka, kasancewar su maza in dai suka taru a waje to fa sai surutun nan ya cika waje komai wayewar su Ita dai bata yi gigin bi ta baban falon ba tana murmushin Salima da ta taho dauke da butar shayi Alamu ta yi mata da ta mahaukacin haduwa, sannan ta mata alamun zasu hade wai motocin MALIK sun karaso na zata iya tsayawa ba ya ritsata a tsaye Ita kam sai ta rasa to ina zata nufa? Ta koma ne har ya shige ko kawai ta yi tafiyarta? Tunawar da ta yi na lalle ya biyo ta wajen karamin falo na ya saka ta karasawa karamin falon , domin shi baban falon akoy hanyar shigarsa, shi yasa ta tafiyarta hankali kwonce tana kallon ABDALLAH, wanda hakan ya sa ta ji kamar hankalinta na neman tashi dan irin ramar da ta ga ya yi A lokacin da take ta kokarin daidaita kanta tana gannin yadda ya wani zuba mata ido yana sauke mata murmushi mai ratsa zuciyar nan hannayensa bude dan kawai ya tsokaneta domin yakan yi mata haka sai ya bude hannayensa yace ta zo, ita kuma sai ta toge tace ta ki din sannan ta bi shi da harara, hakan na matukar saka shi nishadi Hannayensa a bude, yana murmushi ya ce" zo jikina masoyiyatah...." A lokacin da take shirin sakar masa harara gabanta ya kwonci kwonci ya fadi, sakamakon shigowar da MALIKI YUSUF BINE BELLO ya yi, kuma idannuwansa tsai a kansu, kallo irin ya kalli Abdallah wanda ganninsa ya saka shi fadada fuskarsa da murmushi ya mike tsaye dan girmamawa a gare shi, domin dama sun san junna yana siyan manyan motoci a wajensa sai dai basu da wata mu'amala ta kusa da kusa , ko siyan motar wata mota ce da ya so sosai shi kuwa ya ki saidawa sai Honorable ya saka baki ya saida masa ita......... A hankali YUSUF ya dan so lumshe idannuwansa, sai dai wani irin zafi da sukar da suka masa ya hanna shi abinda ya yi niya har ya sake bude su tarrrr a saman fuskarta da ta nuna alamun damuwar da bata san ko ta meye ba har ta dan dago da sauri zata yi magana ta ga ya kauce fuskarsa daga barinta ya maida wajen ABDALLAH da sam bai san abinda yake faruwa ba domin hannu ne ya miko masa dan su yi musabaha Idannuwansa ya lumshe a hankali bayan ya kalli fuskarsa, a nutse ya ......... Happy juma'at Azl 31 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo Idannuwansa ya lumshe a hankali bayan ya kalli fuskarsa, a nutse ya fitar da hannunsa daga cikin alkyabarsa mai dumi ya amshi gaisuwar Barka da zuwan da yake yi masa, sai dai yana amsawar da dan sakin fuska ya shige ciki cikin takunsa yadda ya saba, ba zaka taba cankar halin da yake ciki ba a haka, domin sam bai nuna abinda yake ciki ba, kai zaka iya cewa babu abinda ya gani har ya bacewa ganninsu yannayinta ya nuna tashin hankalinta a bayane har ta zauna ta dafe gaban goshinta ranta na kuna da dan yannayin damuwa da gannin damuwarta ya karaso kusa da kujerar ya zauna yana fadin" Angel, me yake faruwa?, ko na yi laifi ne?" rai bace ta dago dubanta tana dubansa ta bude bakinta tana fadin" Na sha fada maka, a nan kasar Hausa kake, na fada maka bayan kasar Hausar ka hadu da wace bata dauki haka matsayin abinda ba laifi ba, ko a larabawan kunna rungume wace ba muharamarku bane? Ni ba muharamarka bace tunda babu wanda ya shaida daurin aure a da kai, me yasa kake son zubar min da mutunci a wajen da aka dauke Ni ake son bani daraja ne? haba dan Allah, yanzu me kake so ya kalle Ni da shi?" fada ne take yi kamar wanda ya wuce misalin bacin ranta, hakan ya sa ya zuba mata ido har ta dasa aya sannan a sanyaye ya furta" Ki yi hakuri, ban san hakan zai bata maki rai ba, kuma idan kina so sai na nemi alfarmar ganninsa na fada masa tunda kike hakan bai taba shiga tsakaninmu ba, hasalima ina maki haka dan na tsokane ki ne, Please ki yi hakuri" yannayin fitar amon muryarsa da yadda ya hade hannayensa yana bata hakuri suka ankarar da ita abinda ta aikata a hankali ta lumshe idannuwanta, wata matsananciyar Kunya na lulube dukkanin gaban jikinta da kofofin hancinta da idannuwanta ko ba komai ABDALLAH ba yaro bane, kuma kamar abin ya sakata a fushi fiye da misali, domin sai da ta rufe bakinta bayan ya shiga bata hakuri a cen kasan zuciyarta ta ringa tunanin me kennan? ita dake rayuwa da dukan kirjin cewa in dai Allah ya yarda da ita duk wani wanda zai ki yarda da ita ya jima bai ki yarda da ita ba shine zata damu dan wannan mutumen ya wani yi mata kallo kamar ya kama kwartuwa? Kai koda yake walahi bai iya kallo ba, wannan kallon nasa sak irin wanda za'a yiwa wace aka kama da kato ne! A hankali ta dago dubanta gannin Abdallah na kokarin sake bata hakuri da muryarsa dake karyar mata da zuciya, baban mutun irin wannan, mutun mai alfarma sosai a rayuwar yau da gobe? a hankali ta dan zuba masa ido, yadda idannuwansa suka rine da abin ciwo da kuma tashin hankalin dake neman damunsa na ya bata mata rai, dan a rayuwa kwarai yana kiran damuwarta tashin hankalinsa dan haka din ne, sai ta ji tausayinsa ya kama mata zuciya a hankali ta sakar masa murmushi tana kallonsa kasa kasa ta ce" Ka gani ko? ba nace maka mu a nan idan mace na dagawa namiji murya marinta yake yi ba? me yasa kake kyaleni ina daga muryana sama da naka?" shi dinma murmushin ya ji ya kama shi, yana kallonta ya ce" Anya kin san so kuwa?, na tabata da kina jin abinda nake ji a kanki, da ba zaki taba tunanin Ni zan iya saka hannuna a jikinki ba, yayama zan iya dukan mace sai kace mahaukaci? ba'a dukan mace, mace tana da daraja, duk mai dukan mata jaki ne, jahili ne, mahaukaci ne, dan bai san abinda yake ciki ba!, ba zan taba iya aikata hakan ba because i love You so much " RAUDA ta sada idannuwanta tana jin sunna ciko mata da kwallah, ita kam me zata cewa wannan bawan Allahn? me zata fada masa ne? a halin kura ya santa, domin a ranar da suka fara haduwa yana bata kudi ta karɓe ta gudu da nufin ta ci banza har tana iƙirarin ire irin su su kama yar mutane su lalata ne a kan yan kudaden da basu taka kara sun karya ba....sannu a hankali ya gwada mata itace bakuwar kudi, shi ba wannan ya kawo shi ba muryarta a sanyaye ainun tana kallon fuskarsa ta furta" Abdallah yaya zaka ce ban san so ba, bayan i love You too???????" idannuwansa ya tsura mata a hankali ya furta" Da gaske kina so na ?" RAUDA ta yi murmushi dan yadda ya yin ya bata dariya sosai Kai ta sada a hankali ta gyada masa ta shiga wasa da yan yatsunta tana tambayar zuciyarta to mema zai hannata son sa? ai wannan din shine daidai da RAUDA shine daidai da zamanin RAUDA a tausashe bayan ya dan sake matsowa dan daf da ita kadan ya furta" Alhamdulilah, kin san ko yanzu take so ta buga!, ta samu farin ciki, yau kin fada min kina so na, alhamdulilah, abinda ya rage min mallakar ki, ki fadawa Mah a bani abata mu tafi, ki sanar mata ta taimaka min na mori lokacin da nake da shi da wace nake so, Please ki min wannan aikin " RAUDA ta dan zarro ido tana dan matsawa dan bata so sunna irin zaman nan ta ce" Wannan kam Ni dai ba aikina bane, abinda na san aikina ne idan an tambayeni Rauda kina son dan saurayin balaraben nan? Sai na ce na'am ya ummmih......" Dariya ya kubce masa wace ya jima bai yi ba, har yana nuno mata hannunsu dan bata daina bashi dariya idan tace masa dan saurayi, yakan yi dariyar hakan sosai ...... da wannan firar suka samu zuciyoyinsu suka yi sanyi, sannan bai dauki lokaci ba da kansa ya nuna mata zai tafi dan sun gama magana da Mah, ta sanar masa in sha Allah da zarar sun yi maganar da BAH , ko da MALIK za'a neme shi dan bincike sannan a saka ranar aure, dan itama ba laifi ya birgeta tana fatan ya rike mata yarinya da kyau da amana dakin Mah ta nufa ta sanar mata zai tafi, Mah din ya fito suka yi salama sannan ta nunawa RAUDA ta je ta taya Salima kula da bakin yayansu, hakan ya sa ta tafi shima ya wuce ba tare da Mah ta yarda ta yi masa Rakiya ba, Mah dakinta ta koma ta yi kwonciyarta, ita kuma RAUDA ta nufi wajen da muryoyin maza ke tashi sunna dan zantawa ta ja ta tsaya tana tunanin shiga ko komawa? dan kwallin nan ta warware ta yafa saman kan nata, sannan ta saka hannunta ta tura kofar ta madubi ta baban falon wani irin sanyi ne ya yi mata bismillah, sai kanshin turarukan da ta kasa gane wane ya fi dukan zuciyarta, na wutar da ya gama kama ko'ina ko na ruwan , ko na bakin da suka gama garwayuwa suka bada kanshi daban kasa duban mutanen falon ta yi, abu daya ta gane shine matan na gefe ne mazan na gefe, tafiyar ta mata da maza ce kennan, bayan wannan sai Muryar Salima da ta yi kiranta kasa kasa sosai domin dama itama tamkar tana cikin kaya, ji take yi wajen ya girmi tsayuwarta, sai dai kasancewar ya nuna baya son bayin gidan su kula da bakinsa dole ita baba kuma kanwarsa ita zata kula da su din, domin Mah na gannin sauran ta ki turo su ta tabbata da dalili a sanyaye ta karasa kusa da Salima dake saka kankara da abin daukan kankarar a cikin baban jug na kwalba sai da ta cika shi sannan kasa kasa ta ce" Gwara da Allah ya kawo ki, dauki wannan bari na dauko sauran kofunnan mu kaima matan, na gama kaima mazan" RAUDA bata ce komai ba ta saka hannunta ta dauka suka nufi wajen matan nan suka kai suka ajiye Salima ta fara zubawa , RAUDA na saka kankarar suka ji murya a tausashe sosai an furta" RAUDA?" Da sauri RAUDA ta dago kanta, domin Muryar nan ai ba Muryar da zata bace mata bace koda a cikin mafarki ne idannuwansu ne suka sarke da junna ita da Bara'atu da sauri ta dan zarro ido, itama da ta furta sunnan da wasi wasi, dan bata ga abinda ya haɗa RAUDA da ahalin nan ba, bata taɓa kawowa ranta zata ganta a nan ba, ta zarro idon wannan karron da dan karfi ta furta" RAUDA?, KE CE" RAUDA ta lumshe idannuwanta, da sauri ta ajiye abin saka kankarar idannuwanta na tara kwallah tana kallon ATU mikewa Atu ta yi tana ajiye wayarta saman kujerar nan ta karaso da sauri ta kama hannun RAUDA ta nufi waje da ita Salima ta raka su da ido, tana son bin su ama tana tsoro, sai da ta ji mijin Rauda din na fadin" Ikon Allah biya Muradi dama aminiyar aminiyata na gidan nan muka yi ta nemanta?" YUSUF dake zaune cikinsu, kansa tamkar ya fashe masa dan tsananin ciwon da yake yi masa, jikinsa kuwa zafi ne da shi na gasken gaske, idannuwansa a lumshe suke tunda ya karaso ya zauna, tun sunna tsokanarsa cewar dama yaya lafiyar kura Balantana ta yi hauka? har suka zura masa ido suka ci gaba da firarsu dan sun zo walahi bai isa ya kore su daga zuwansa ba, a cikinsu da yawa na son zantawa da shi, ama sai hakura suka yi dan ƙarara alamu sun nuna ba zai iya doguwar firar ba, in dai ya ji suturun ya yi yawa ne yake bude idannuwansa ya ringa binsu da kallo a ransa yana ayana' kartin banza kun zo da matanku kun wani saki baki sai surutu kuke yi, na zaku dan ringa daidaitawa ba, an girma sai shirme!' sai dai bai furta a bayane ba, ya dai yiwa kansa alkawarin sai ya turawa kowane wannan sakon idan ya so su dawo su cinye shi! sunna fitowa ta nufi karamin falon da suka bi ta ciki suka karasa baban da Rauda sannan ya cika hannunta da karfi ranta bace tana bukatar da yatsa ta ce" Dama kina raye? kina duniyar? ama kika kasa daukan waya rana daya ki yi kirana ki ji muryana? Ni da na damu da ke shine nake sunturin neman inda kike? tunda na je wajen mama tace min bata san inda kika shiga ba har a asibiti aka kwontar da Ni dan damuwa? ke shikenan ba zaki taba mayar da Ni yar uwarki kamar yadda na mayar da ke ba? kina cikin Nijar zuwa inda nake ya gagare ki? alhamdulilah tunda kina nan raye kuma lafiyarki kalau, nima daga yau zan cire ki a raina na hakura da zumuncin tunda bakya so!" Atu ta karashe tana fashewa da kuka, dan walahi Allah kadai ya san yadda ta dauki Rauda a ranta, a lokacin da ta ga ta yi sati Uku cif a gidan miji ba Rauda ba labarinta sai ta shiga nemanta, ta daina fushin ta ringa neman layinta, ama bata samu, nan ta shiga daga hankalinta da na mijinta, ama a banza, sannu sannu har ta yi wata biyu a gidanta sannan ta tada hankalin kowa har ya dauketa suka je gidan su Rauda din, a nan ne Mama ke ce mata bata san inda take ba!, kamar da wasa har sai da ta sha karin ruwa dan tunani da damuwar ina Rauda zata je? ina zata je jama'a? domin a duniyar Rauda babu abinda bata sani ba, idan har Rauda ta bata , bata san inda zata nufa ba kuma hankali Tashe RAUDA ta karaso inda take kukan nan da sauri ta riko hannayenta itama hawayenta na zubowa daga gurbin idannuwanta murya a raunane ainun ta ce" Haba Atuna, dan Allah kar ki yi fushi da Raudanki, idan kika yi fushi ina zan saka kaina ne?, ke kin san ba dai maganar bana son zumunci da ke ba, idan ban yi da ke ba to wa zan iya yin zumunci da shi? kin fita daga sawun kawa kin jima da zama yar uwata, walahi na cire layinmu da muke magana da ke ne saboda na yiwa aunty biyayya, kema a yanzu da kike wuyan wani so kike a ci gaba da irin na jiya? kin yi aure Atuna, baban burina ki zauna kalau a gidanki,ki fuskanci rayuwar aurenki, ki zauna lafiya da mijinki, so kike yi kulun na kwaso na zo mu wuni muna shirme har ki kasa kama darajar da ya dace ki kama a wajensa ta hanyar shinfida rayuwar da ta dace a tsakanin ke da shi? kin manta me muka ce? eh muna iya auren mai mata, kuma muna iya shafe karatun da ya jima yana dauka daga wajenta in dai ba yadda ya dace ta bashi bane? dan Allah ki tausaya wa aminiyarki ki yafe min...." ATU na kallonta, ta tabata wayon da ta saba yi mata dan ya sauko idan ta yi fushi take yi mata, sai dai na yanzun ya matukar taba mata zuciya tana kallonta murya a raunane ta ce" Wace aunty ce zaki yiwa biyayya?, me kike yi a nan? Tun yaushe kika zo? dama kina da alaka da MALIK YUSEF NE?" wajen kujerar da suka gama fira da Abdallah ta ja ta suka zauna, a zuciyarta tana tunanin me zata fada mata dangane da tambayar wace auntyn da ta yi mata?, sam ba zata so ta cewa Atu kanwar mahaifiyarta ta ja mata kashe da hulɗar dake tsakaninsu, ta fada mata ruwa fa ba sa'an kwondo bane, ta nuna mata kwadayin da take yi ya dace ace ya koshi dan ta samu wanda ta samu a tare da ATU, ta shaida mata yanzu Atu darajarta ta karra daukaka ya dace ta bata lafiya ta yi zaman aure? Kai tana gannin maimaita wannan kalaman ma Atu wani tashin tashina ne da batawa kai rai a banza a wofi, domin duk abinda kanwar mahaifiyarta ta fada gaskiya ne, zaren ba kalar yadin bane, shishigi kuwa bashi da wani anfani, kuma ba laifi ta ginu da taimakon Atu ba zata yi karyar haka ba a tausashe tana kallonta ta ce" Azl 32 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo a tausashe Rauda na kallonta ta ce" Wane kike son ji a ciki? ho Atu maimakun mu yi ta murnar gannin junna shikenan sai rigima?" Atu ta ce" Kowane ina son ji Malama ba wani, kowane ina son ji!" RAUDA ta yi murmushi dan ta tabata Atu zata nemeta dama, sai dai ta dan bata waje ne dan itama ta huta da zagin da wasu cikin ahalinta ke yi mata, tun sunna zuwa makaranta tare wani lokacin cikin yan uwan atun da suke uba guda zaka ga ana yada mata magana, ko idan an zo shiga Mota sai su baje ace ita ta shiga Boot, sun sha shigewa Boot din ita da Atun dan idan tace zata zo a kafa sai Atu tace itama zata zo a kafa, direba ke kiyawa dan ba zai taba kai Yaren gidan babu wata ba, kuma har ga Allah shi bai ga abinda RAUDA ta yi masu ba, ga waje nan su ce babu, idan ya dauke kafa ya nemi kin zuwa inda take ita sai ta zo inda take din, a dole ta hakura da duk wata kyara da hantara da gorin arziki ta toshe kunnayenta ta rintse idannuwanta dan ta riga ta gane ko me zata yi ba za'a raba zumuncinsu ba, sai kawai suke tafe a haka a tausashe ta ce" Na jima a nan ai Atu, tun ranar da aka naɗa shi sarauta muka zo nan, kafin a nada shin kuwa na kwana ɗaya a wajensu, a takaice dai su din iyayen marainiya ne, mahaifiyarsa ce ta daukeni, mahaifinsa yace ya ji ya gani, shine suke rike da Ni" Atu da jikinta ya fara wani irin masifar sanyi tana kallonta ta ce" Kamar yaya suka dauko ki? me ya same ki a gidan uncle din? " ajiyar zuciya RAUDA ya sauke, a sanyaye ta shiga labarta mata abinda ya faru, tun daga batan Uncle, har zuwa sace Abdul da abinda ya wakana bayan hakanan" a hankali Atu ta saka hijab dinta ta rufe fuskarta tana girgiza kanta dan kukan da take tarewa da kyar ta iya sasautawa tana kallon RAUDA dake fadan ta daina wai meye na koke koken? ATU ta ce" Shine kika ki zuwa inda nake? shine kika ki dauke Abdul ku zo wajena?, kin san ko baki zauna a gidana ba kina iya zama a wajen Hajia ko? kin san Hajia na son ki domin Allah ko? shine ko ko tuna Ni kika yi tafiyarki kin samu Mah da wancen kanwar HONORABLE din ko?" RAUDA ta yi murmushi tana fadin" ke kam ba dai jaje ba, to wai ki yi hakuri mana, sai da na daina baki hakurin ku ji min mata!" itama yar dariyar ta yi tana kallon Salima da ta shigo yana murmushi ta ce" An ce fa ki je ku wuce, tuni sun fita sauran sun tafi ma" Atu ta mike tana fadin" Bari in fadawa dear ya BARNI na kwana a nan din nima ko ki zo mu tafi" daga Salima har RAUDA ido suka zarro, da kyar suka rarasheta bayan ta amshi numbar Salimar tana fadin zata dawo ta kawo mata wata wayar kuma su tafi tare idan ta fadawa Mah ita dai Rauda murmushi kawai take yi, suka rakata har wajen mota sannan suka dawo sunna shigowa falo Salima ya amsa kiran mahaifiyarta, tana kallon RAUDA ta ce" bari ki ji, walahi wanke wanke na jiranki dan na kai maki su na tara maki, idan na fito daga dakin Mama daki zan wuce na yiwa Abdul lesson nima na yi karatu ehe!" tana fada tana yin ciki da dan gudu ne, hakan ya saka RAUDA sakin murmushi tana girgiza kanta ta nufi kicin din hankali kwonce ta cire dan kwalin nan ta rataya ta daure gashinta a tsakiya sannan ta shiga gyara plate plate din wajen pampo ta dauko sabulu da sponge ta shiga wankawa zuciyarta fesss, ta samu duk wani nauyi ya ragu sai nishadi take ji a cen kasan zuciyar Tata, ko dan ta hadu da ATU ne? ko kuwa dan ta samu nutsuwa a fira da Abdallah ne? ita dai ta fi jin dadin a cen kasan zuciyarta idan ta waiga ta waigo ta ganta tsaye itama ana bata ba tare da an yi mata gori ba, ana ciyar da ita ba tare da ance ta kawo kasonta itama ba, ana yin fira da ita tamkar wata mai cikakken yanci, tana motsawa yadda ta so da tunanin kiran wata Mama har cikin ranta bayan Tata uwar ta kwonta dama, bata taba tunanin bayan gawarwakin da aka barta ta hanga daga nesa zata kuma jin ana yi mata fada dan ta gyara ba, dan a da ta yarda cewa tunda aka birne iyayenta shikenan an birne mai sakata kuma bai hannata, ashe a duniya akoy wa'inda ke daukan dan wani tamkar nasu har su yi masa fadan rayuwa? zata ci gaba da godewa Allah dan shine ya yasare mata har ta samu wannan daukaka tana aikinta da bege ne a zuciyarta har ta juyo dan daukar abin goge kofunnan nan na kwalba dan ya rataye su a jikin karfen da ake rataye su idannuwanta suka sarku cikin nasa, da sauri ta rintse idannuwanta kasa kasa ta dafe kirjinta da ya buga mata da mugun karfi ta furta" A'uzubilahi minna shaidani rajim" kofar frij din dake hannunsa ya mayar a hankali ya rufe , yana rike da kwalbar lemun da ya dauko ya karasa saman kujerar dake kicin din mai dauke da dan table, domin irinsu sun kai hudu a kicin din ya zauna yana ajiye kwalbar sannan ya sake dago dubansa ya kuma zuba duban da ya yi mata a dazu wanda ya gama raya mata sak yana mata kallon wata fasika subahanallah idannuwanta ta dauke, dan bata iya irin kallon nan ba, da wahala ta iya jurewa, ama kuma ta kasa jure kawar da kan nata da kuma kasa hakura da abinda ranta ke ayana mata har ta sake juyowa ta kalle shi zuciyarta na dokawa tana jin tamkar ta je inda yake zaunen nan ta fada masa walahi abinda ya gani ba abinda yake tunani bane a kanta, ama ta kasa dan haba daya yakan cike mata idannuwa da tunani ne har ta ji ta gaza katabus idan yana wajen idannuwansa ya cire a kanta, yana jin dacin da ya rike masa makogwaro har yanzu bai fada ba, shi yasa ya fito daukan jus dan baya bukatar surutu da kowa sai gashi ya samu yar nan a kicin din tana aiki , shi dai bai san me ya zaunar da shi ba, ya dai zauna ne ya kasa tafiya karasawa ta yi ta dauki abin bude juss din, sannan ta dauki kofin da ta wanke jiki a mace ta karaso wajen table din ta ajiye kofin hannunta na dan so ya mata rawa dan har sai da ta dan jimke shi kafin ta kama kwalbar da abin budewar nan ta bude sannan ta dan dago a hankali idannuwanta suka sake shiga cikin nasa daburcewa ta yi , a sanyaye ta ce " walahi ba abinda kake tunani bane a kaina, Ni ba yar iska bace, kuma shima hakanan, barkwonci ne da tsokana take saka shi yin wasu ab....." sai kuma ta yi shiru tana haki tamkar an biyota da gudu kaifafun idannuwansa kawai ke kanta, ci kanki bai furta mata ba ya dauki jus din ya fice, inda ta ji wani shayinsa da tsoron yannayinsa a ranta, wanda bata taɓa ji ba, tunda Allah ya haliceta, bata firgita a kan laifin da ta san ta aikata bale wanda bata aikata ba , a birkice ta zauna saman kujerar tana yamutsa gashin kanta, tana jin tausayin kanta, kai abinda ta sani daya ne kar ya fadawa Mah wata maganar da Mah din zata ji haushinta, dan bata san me yake iya fasarata ba, dukda ya san da wahala ya wani kula da abinda ya gani, ama kuma idan da bashi da wani nauyi a kansa, yanzun yana da shi, dole ire iren abubuwan nan ya taka masu birki a masarautarsa yana komawa dakin ya nemi waje ya zauna yana kama sunnansa a cikin zuciyarsa lokaci guda yana fadawa kansa magangannun da suka yi tasiri sosai wajen nesanta shi da AZAL!, ya fada tun kafin ya gane kansa, bayan ya gane kansa kuwa ya fada babu AZAL din da ta wuce ya *SOYAYA!* , kuma in sha Allah shine da kansa zai yi yaki da kankin kansa ɗan gannin bata shafe shi ba, ba zai taba yarda da wannan *AZAL* din ba, komai rikicinta kuwa zai ture ne, dan haka ya kafa kai ya shanye jus din ya dauko wayarsa ya fara shiga sakwannin da aka ajiye masa na karin binciken da yake yi da irin tsarin da *TASA SALON SARAUTARSA* yake so ta kasance wannan suka dan dauke masa hankali daga abinda yake tunanin ba'a kyauta masa ba, har ya dawo ya ringa basarwa tamkar babu wani abinda ke iya Dada shi da kasssssss a wannan fannin, dan binciken da TAJ ya masa a kan matar nan da Mah ke fushi da ita ya sake dauke masa hankali, wai ya je ya samu an yi mata sata, kuma bata san inda y'arta ta shiga ba, hakan ya sa tana neman susucewa domin zancecekun da take yi sai ya dauki fansa, ko a kan wa take nufi bai gane ba shi dai, ama kuma baban abinda ya fi ganewa shine babu abinda ke girgizata irin maganar mijinta da ta y'arta,da wannan ya rufe bincike bincikensa bayan ya ji jikin Uncle Umar ya warware sosai likitan na saka ran sakinsa nan da yan kwanaki idan ya sake murmujewa ciwukansa suka yi sauki sosai. "Ashe baki da wayo? ashe shashasha ce ke?, uban me kike yiwa rawar jikin da zai sa kulun kina gindinsu? kin kawo su dakinki sai wahala kike ɗorawa kanki? Tun ina kauda kai har kin sa na magantu ke baki da hankali ne? Salima bari ki ji Salima A ruwa akan dade ba a wuta ba, kuma duk abinda kike tsinta a wajensu na soke ba ke ba YUSUF bale tarkacen dake tare da duniyarsa!" mahaifiyar Salima ke yi mata fada tunda ta shigo ta duka a gabanta rai bace ta dora da fadin" kina kallo, tunda suka zo uwarsa ta kange komai, da gidanmu ama Hajia ta zo ta shinshinfida mana dokoki dan an dora dan so a mulki, a yi mu gani in tusa zata hura wuta, in dai mashayin yake kuma mazinaci? Sai ya aikata a cikin gari ta yadda zamu fito mu jefe shi!, ke dai ina hanna ki shiga harkar su, ina maki hannunka mai sanda har kin saka na yi maki magana, ki guji ranar da raina zai bace walahi sai kin kasa gane Ni, dan ba zan taba sasauta Maki ba!" Kan Salima na kasa ne, hawaye na bin fuskarta, a zuwanta dakin mari biyu ta sha kafin wannan tashin hankalin ya biyo baya....., ba marin ne ya fi daga mata hankali ba irin furucin bakin mahaifiyarta shin me ya yi zafi ne? me yasa ake son kai abinda yake danko da danko gaban wuta dan a raba? jinni daya fa akace, a jinni dayanma uba ne shi, ya kyautatawa kowa da kowa ba wai iya su da suke kannensa ba a raunane sosai ta ce" Mama dan Allah ki yi hakuri" Mahaifiyarta ta dauke kanta tana tuna sharar shanyen da kishiyarta ta yi mata dazu , cikin dariya wai tace su Salima dai kiri kiri an zama boyi, a yi girki a yi gyaran gida , koda yake ta yi abinta ita ta san abinda ake bata, maganar ya mata zafi sosai, kuma ta kasa magana dan gaskiya ta fada, Salimar ta zama kamar waya boyin gidan, komai ita ke ja da sauran yan matan, itama abin nan na yi mata ciwo, ama ba komai ai zai dawo gidan shi Hon din, idan ya dawo a san abinda ake ciki, ita ta dukufa ne addu'a take yi yana dawowa ya amshi mulkin nan a ga ta tsiya, sun ga ta isa da takama daga Hajiar har ANDIYAR , dukda Honorable dinma nasun ne ama ba su kadai ba harda suma da ake yiwa gani ganin! "ki tashi ki je ki yi abinda zai gyara ki, fitowarki a babar likita shine tsirarki a kulun ina fada maki, mace kike in baki jajircewa kanki ba haka zaki yi rayuwa a bayan wasu!" jiki ba karfi, zuciya a mace murus da zafafan kalaman dake fitowa daga bakin wace ya dace ace ta fi kowa taushi da sanyayawa, koda zafi ya kora ya dace ace an ji sanyi a karkashin ta sai gashi yauma da ta samu damar fakewa da wani fushin ta dandankara magangannun da bata sani ba sun jima da yin miki a zuciyar y'arta, sun matukar nisanta ta da yarinyarta , domin da tana da kula da ta gane babu wani abu dake shiga tsakaninta da yar da ta haifa da ya danganci na rayuwarta, sai wanda ya zamo dole ta sani...., ta rasa babar damar da ya dace ace itace ke rike da ita ba kowa ba a hannunta fitowa ta yi tana share hawayenta, sai dai kirjinta ya riga ya rike mata, da dan sauri ta nufi baban falon dan ta san yanzu kam ba kowa a cen tana coshe bakinta tana shiga ta barke da kuka da take tarewa da sauri ta nufi kujera zata haye ta darji kukanta ta ga RAUDA a dukunkunne tana nata kukan harda shasheka da sauri suke goge hawaye, RAUDA na kallonta, itama tana kallonta da kyar ta ja numfashi ta ce" Ke kuwa ke da wa kike kuka kuma?" Salima ta dan sake zuba mata ido ta ce" Ke zan tambaya ke da na bari lafiya kalau?" zaunawa Salima ta yi tana sauke ajiyar zuciya suka shiga fira, fira ta rayuwa, sama sama, firar kame kame dan su kawar da damuwarsu, har suka cika dare sannan suka wuce daki, da fatan samun barci, domin ita damuwa a riketa a rai ta fi haifar da ila da karancin barci. ...................................................... *washe gari* tunda duku duku suka wuce asibiti wajen Bah sun same shi zaune saman salaya yana jan carbi, a yau har ya samu ya yi sallah da kansa a tsaye kuma, sannan ko fuskarsa ka kalla zaka gane cewar sauki fa ya samu sai godiyar Ubangiji, hakan ya sa suka zauna Mah sai labari take masa shi kuwa yana biye mata yana ta faman dariyar na dariya, labaran da ba zasu wuce na Hajia, na YUSUF, na RAUDA, Salima, Abdul, da dai duk wani dake tare da su MAH na murmushin gannin Bah na fadin shi dai yanzu tare zasu juya, YUSUF yace ba inda zai tafi sai ya warke sumul shi kuwa yana faman fadin ya warke me ya yi saura kuma, ama YUSUF ya yi shiru yana girgiza kafa ta ce" Aban YUSUF , gwara ka yi hakuri, dan nima na fi so ace komai normal sai mu je gida, abinda ka samu lafiya, ka ga zuwa lokacin jikin baban RAUDA shima ya warware sai kawai a sha bikinta dan ka ga jiya mun zauna da mai neman auren nata, kuma har ga Allah bashi da laifi, Aban Yusuf ka fa san mutumen nan, ina balaraben nan dake yawan sakawa ka cema Yusuf ya saida masa mota?" YUSUF ya dago idannuwansa a hankali ya sauke saman Mah, shi dai bai san cewa baki na furucin abinda ba'a saka shi ba sai yau, domin yana ji yana gani sai ji ya yi ya ce" Dama maganar har ta yi karfin da za'a aura mata shi?" Mah dake diban abinci a spoon tana yin bakin Bah da shi, shi kuwa yana wani karbewa kamar wanda baya iya ci da kansa ta kalle shi ta ce" Azl 33 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo ta kalle shi ta ce" Eh fa, ya yi, kuma tana son shi, Ni dama abinda ya dameni kennan, yanzu abu daya ne nake so dan Allah a maida hankali a kai, a yi bincike, dan ko dan gari ne ba zan bashi y'ata ba bincike ba, bale bako" Bah ya yi murmushi yana rike hannunta da ta nufi shi da abincin ya ce" In dai Abdallah Balarabe kike nufi kar ki damu Hajia, dama na san shi dan har tushensa na je, ama zan binciko me ya zama yanzu dan dan adam akoy cenza hali, ki ce bana akoy sabga a gabana zan aurar da y'a " y'ar dariya Mah ta yi, tana kallon YUSUF ya fice a dakin ta ce" ba karamin aiki ba Bah, domin ko kayan daki Bama son na gida na waje muke so!" A lokacin da Mah ke fira da mijinta YUSUF ya fito coridor din dakin da Bah ke ciki ya yi tsaye ya saka hannayensa cikin aljihun rigar dake jikinsa ta jalabiya ya yi tsaye yana dan hangen mutane daidaikun da wani dalili ke fitar da su mai karfi daga dakunnansu domin tunda ya shigo aka dakatar da kowa aka fada masu na dan lokaci ne yanzu zai fita , hakan ya sa polisan dake tare da motarsa shi da Mah suka dan bazu sunna kai kawo da tarar duk wani wanda zai shigo ko zai fita Bai san adadin lokacin da ya dauka ba, sai da Mah ta fito tana fada masa babansa na kiransa, ita ta tsaya a waje shi kuwa ya shiga ne ya ga ashe sun jima sunna shan firar su yan soyaya yana shiga Bah ya zuba masa ido yana fadin" zo nan" YUSUF ya kalli inda ya nuna masa sannan ya karasa ya zauna yana hade hannayensa yana kallon BAH Bah ya ce" Me yake damunka?" YUSUF ya sake zuba masa ido ya ce" Ni?" Bah ya dafe haba yana kallonsa ya ce" Honorable Ni, nace Ni, ka ga ka rufa min asiri kar na daki sarki fa?" murmushi ya subucewa YUSUF, shi kuwa BAH ya yi yar dariya yana kallonsa a tausashe ya ce" Ka ci gaba da hakuri , in sha Allah na kusa dawowa kusanka, zan tayaka kokawar nan, bi izinillah zaka kai ga cin nasarar rikon kasarka, ok?" YUSUF ya lumshe idannuwansa sannan ya sakarwa mahaifinsa murmushi yana kallonsa ya ce" Allah ya aminta" Bah ya amsa da amen sannan suka yi salama suka nufi gida sunna karasawa gidan shi dakinsa ya wuce, Mah kuwa har zata kwonta itama hayaniya ta shiga shiga cikin kunnayenta, kuma hayaniyar da bata saba ji ba a sanyin safiya irin haka, domin yawancin lokuta sukan fice ciki koda fira zasu yi su Dukansu yan matan dan saurarawa ta yi, sai ta ji ai kamar kuka, hakan ya sa ta mike da sauri tana daukan hijabinta ta saka ta fito da dan sauri ta nufi ciki dan sarai ta ji mamakin gannin ba a falo suke ba ashe sunna cen dakin SALIMA da sauri ya tura kofar ta shiga da salama tana sauke idannuwanta kansu, lokaci daya ta shiga tafa hannu a tausashe ta furta" Subahanallah, menene wannan din, ke Musulima rikewar me ake yi maki? kin ga Salima saketa , kai saketa ku saurara min, meye haka, menene wannan kuke yi kamar wasu mararsa ilimi?" sakin nata Salima ta yi tana haki dan walahi sun jijigata, RAUDA kuwa tunda ta ji ba'asin rikicin nasu ta ja tana kallonsu shi yasa rabiyar fadan ya dawo kan Salima ita kadai Rai bace Mah ta ce" ku zauna min, a'a, me ya haɗa ku da junna kunna yan uwan junna fada harda dukan junna? ashe baku da tunani? yaushe rabon duniya da fada bale wai har a daki junna? meye ya haɗa ku da zafi haka wanda ba zaku iya tattaunawa ku ba junna hakuri Ni Ameera jikar Ameerah sai dambe?" Akilah ta sake sada kanta zuciyarta na tafarfasa Hindatu da suka sakata a cikin rigimar dan kawai tace masu meye na fada in dai a kan wannan ne kowa ya iya allonsa ya wanke ce ta ce" Mah, ki' ga wai dan Akilah ta yi create compte a Tiktok ta saka matar Malik shine Musulima ta gani tsakiyar dare, shine yau tunda muka tashi take masifa har sai da ta kula ta suka fara fada, Ni daga raba su ta zage Ni " Mah ta dubeta tana fadin" ku ji 'in wani shirme, waye Malik kuma har da zai hada ku fada da junnanku? yau ko miji daya kuke aure ai inaga kun fi karfin wannan shirmen bale a sanina babu mai aure cikinku? shiru ne wajen ya dauka, kowace ta kasa ba Mah amsar waye MALIK har sai da ta daina jiran jin waye Malik din ta aniya fada tana fadin" Yaushema da darajarku da komai, kunna cikakkun yan mata zaku tsaya kan saurayi kunna fada? waye shi Malik din? to ko waye ba ku ba shi tunda ya iya rashin mutuncin yin soyaya da yan uwan junna a tare " Salima ta dago tana kallon Mah ta ce" Mah, yayanmu ne fa, a kansa ne suke fadan, su Dukansu ukun ne suke yin fadan a kansa ne kuma!" gaban Mah sai da ya fadi, wajen kuwa ya yi tsitttttt dan kuwa Mah dake hakilon fadan nan sai bakinta ya yi tsittt lokaci daya tana kallon su ta jima a haka ta kasa furta ko a, ta kalli wannan ta kalli wancen ciki harda Salimar da RAUDAR kasa kasa tamkar mai rada ta ce" Soyaya kuke yi da shi ne dama ban sani ba?" ta yi tambayar nan ne gabanta na faduwa, dan abinda take iya yin gudun ji daga bakin daya daga cikin Yaren nan shine amsar EH, dan bata tunanin zata iya yarda YUSUF ya auri daya daga cikin ya'yan yan uwanta da ranta da lafiyarta, sai dai idan kadara ta gama zuwa a haka, wace zata zo da rabo........na wai dan bata yafe ba, ta yafe fa, sosai da sosai, kawai dai ba zata bari ta cuce su bane su auri ɗan Yar iska da dan iska! wannan karon ma ba amsa, har ranta ya fara suya ta dubi Salima da mugun hararan da ya saka Salimar bude baki a sanyaye ta ce" Mah, inaga shi fa baima sani ba fa" har ga Allah sai da ajiyar zuciya ta kwace mata, tana kallonsu ta ce" Abinda Salima ke fada gaskiya ne? a kan YUSUF Ne ? Kuma bai sani Bama?" wannan karon Musulima ce ta gyada kanta , kan nata a kasss Mah ta girgiza kanta tana kallon su gaba dayansu ta ce" Yaushe kuka zama haka? ko dama haka kuke ban sani ba su aunty na kallon ku basu tsawatar ba?, ikon Allah da dukan junna zaku yi ta yi a kan abinda ba zai wani yiwu ba? yaya za'a yi mu yarda mu maku auren hadi auren da ba soyaya? ai ba zai taba yiwuwa ba , kai ko da soyaya mu Bama auren dangi dan gudun matsala salon ku zo nan ku yi rikici ku lalata mana zumunnci, Ni koda soyaya kuke yi ba zan bashi ba bale bakwa soyaya, ke maza ki je ki goge abinda kika dora, ke kuwa ku yafi junna ku zubar da shirme, ba soyaya tsakaninku da YUSUF kowace ta samo mijinta na wanketa ba kaita dakinta lami lafiya yadda koda gobe ya yi mata ba daidai ba na daure kugu na zabga masa mari kuma na mari banza ko baby?" RAUDA ta yi murmushin yake ya sake dauke kanta, Mah kuwa ta mike tana sake toshe kwakwaluwarsu ta ce" Kar fa na kuma jin wannan maganar, maza a yafi junna, shima ai da matarsa kowa ya fitar da nasa maza a wanke ku a kai ku dakunan ku!" tashin hankali wanda ba'a saka masa rana, sosai Mah ta daga hankalin ƴaƴanta domin kuwa bata sani bane zaman nan na yakin duniyar YUSUF ne sai gashi tana fadin basa auren zumunci basa son maganar? kowace wayarta ya dauka dan isar da sakon inda ya dace a lokacin kuwa Mah ta nufi dakinta, zuciyarta cike da mamakin abokanan zamanta, anya kuwa mutanen nan ko wuta dakinta ke ci sa fada mata? ya Salam, ace sunna gidan sunna jin wannan katsamniyar ba zasu fito su tsawatar ba?, ikon Allah tana zama bakin gadon ta kuwa sai ta lumshe idannuwanta tana jin barcinma du ya watse a idannuwanta uhum, rayuwa kennan me yan uwanta suke nufi ne? Allah ne masani ama har sun manta a lokacin da ciki ya bilo jikinta, mahaifiyarta ke fadin a zo a hadu a rufawa junna asiri a fitar da ita nesa idan ta haihu ta gyaru sai ta dawo a aura mata cousin dinta, wanda ke sonta kamar me, suka dira suka nuna ina, su fa bama za'a kawo masu auren dangi ba, dan basa son fitina, kowa ya samo mijinsa a waje a aura masa, koda ace bata dauke da wani abin kunya ai ba zasu yi auren zumunci ba bale ita da ta watsa kanta salon Abu ya bude ta yaba masu abin kunyarta, a'a ba zai yiwu ba kawai ta nemo uban cikinta cen su karata....... Kai ta girgiza tana kore tunanin dan kar ya cenza mata mood, abu daya ta sani shine YUSUF itace mahaifiyarsa, ta yanke wannan hukuncin babu mai dawo lata da shi sai idan Allah ne ya hukunta haka babu yadda ta iya! a dakinsu kuwa, a ranar Rauda kadai ta dirki aikace aikacen gidan, domin tunda abin ya faru da ta fito ta shiga aiki bata kuma bi ta kan kowa ba, babu wanda ya san me yake damunta, aiki dai take yi ba sakin fuska, domin Salima ta dan dauke kafa dan sau biyu mahaifiyarta na fitowa dan ta ga in ta shiga aikin gidan ko a'a, shi yasa Rauda tace ta zauna inama aikin yake abinda sharar iya ta nan din ce, da guga sai girki, yan matan kuwa kusan kowace a bangarenta daban ta zauna, bisa kalar hudubar da mahaifiyarta ta yi mata, sunna nan daram a gidan, dan iyayensu sun nuna zasu zo ne da kansu wajen mai sunnan Hajiar, kula kowace ta kalubalanci yar uwarta da jin haushin junna, ita dai wace ake yi dan itan bata sani ba tana shan tana nata shagalin abinda zai fidata! ....................................................... a cikin satin da ya gabata aka sako Bah daga asibiti, ama kuma likitansa bai tafi ba sai da ya rufa kwana na goma a garin sannan ya juya tasa kasar da farin cikin gannin an samu nasara patient dinsa ya warke tunda suka dawo gidan baya rabo da baki, ta ko'ina, ga bangaren guda kuma ana tafka aikin ginnin nan abin har abin tsoro domin aikin an fara shi nan da nan har yana neman shan duka, dan kuwa sosai an cimma aikin , dama yanzu ginni in dai da kudi shikenan kafin kace meye wannan an gama, danma akoy hawa da hawa wa'inda ba'a masu garajen, dole ana bin ka'idarsu dan kar su tafka tsiya ai da tuni an gama aikin, dan masu ginnin nan yan Chaina ne aka dauko ginni ya gama kankama a cikin yan zuwa gaisar da Bah, harda ABDALLAH, wanda ya samu kyakkyawan tarba daga sirikinsa, har Bah ya sanar masa cewa an bashi ama ya yi hakuri a satin gaba za'a salami marikinta, shine mai tabatarwa, su sun nuna masa kauna ne, ama mai bashi babanta ne tunda da ransa da wannan ya sake tafiya da farin cikinsa, dan kuwa har wajen da yake Bah ya sanar masa ya kuma bashi damar ziyartarsa idan yana da ra'ayi a cikin wannan dan tsakin, zukata biyu na tare da gagarumin kadarar da ta rigayi fata wace kowane ya murje ya kane ya watsar dan nasa dalili mai karfin da yake gannin ko waye ya ji zai jinjinawa namijin kokarinsa harma ya bashi kyauta ta jinjinawa da girmamawa tunda suka yi magana a kicin wata bata kuma hada su ba, domin karfi da yaji sun gane zagayewar nan itace alkhairi a gare su ba tare da daya ya gane manufar daya ba, sai baban haushin junna da ya darsu a zukatan na gannin wane bai kyauta min ba ko kuma wane ya yi min ganganci , kowa ya kama kowa da laifin da bai aikata ba wanda ya gama kashe zuciyar bege ta koma ta jin haushi da jiran laifin wani a cikin satin da aka salamo uncle Umar direct fada aka nufa da shi, domin an sallame shi daga jinyar jiki ne, a yanzu ta magance shaye shayensa za'a ci gaba da yi , wace YUSUF ya gama sakawa an nema masa wajen da ake wannan, kwanakin nan da zai yi biyu dan ya san huta ne hankalinsa ya dawo jikinsa sannan ya daga zuwa neman lafiyarsa a wannan rana RAUDA ta yi kukan farin ciki, hakama Baba Umar da ya ga yar amanarsa da kuma d'ansa cikin koshin lafiya, babu abinda ya karra bashi mamaki irin yadda Abdul du wasu alamu na hauka dake nuni a da a tatare da shi sun rage, wa'inda ya gama ganewa eh lalle yaron yana da yar matsala ama bata kai wajen da ta nuna a da ba, tsabar tsoro da firgici ya sa yake tafe a mahaukaci ziryan, a yanzu da yake cikin nutsuwar zuciya, ba zaka ce Abdul bane, harta kalar fatarsa ta haskaka sai hamdallah kasancewar da rana suka tarda shi bai samu zama da RAUDA ba sai da dare bayan sun ci abinci ta sake komawa wajensa, a lokacin ne ya dubeta cike da rauni ya ce" cike da rauni uncle Umar ya ce" RAUDANA, my daughter, dan Allah ki yafe min, ki yafewa babanki, na dauko ki daga hannun wace ta yiwu da a wajenta kike da yanzun wata maganar ake yi ba irin tawa ba, har Allah ya amshi ranta ban bata dama ta baki tarbiyya da ilimi ba, ban san makarantar ki ta islamiyya ba ban san ta boko ba, sama sama idan na dan auna ne nakan kwatanta wasu kulawar da basu taka kara suka karya ba, maimakun na rike ki sai na karra maki rikon wani a kanki bayan ke dinma riko ce, sannan na hadaki zama da macen da sam bata da tausayi bale jin tsoron Allah a lamuranta, dan Allah ki yafe m..,....." "Aba....." RAUDA ta fada a sanyaye, ba dan ta katse shi ba, kuma ba dan maganar da yake yi bata da mahinmanci ba, sai dan ba zata iya jin muryarsa a matsayinsa na uba a wajenta yana bata hakuri a kan yannayin zubin rayuwar da shi dinma ya yita ne yadda ta jirga shi, kwarai tana cikin yannayi, sai dai a yanzu kuma me ya rage mata na fitina? Allah ya gama wanke mutanen kirki daga cikin mutanensa na kirki ya hadata da su, sunna zaune tamkar y'ar da suka haifa da cikinsu, me kuma ya yi saura? a sanyaye sosai ta ce" Dan Allah Aba ka daina bani hakuri, baka taba yi min laifi ba, koda ka min wanda ban sani ba na yafe maka duniya da kiyama ama ka daina bani hakuri, ni yanzun hankalina ya kwonta da Allah ya sa kana raye, ina fatan Allah ya karra tsare min kai a duk inda zaka shiga Aba" hawayen da yake ta tarewa dole sai da suka zubar masa, ama kuma har cikin ransa sai ya ji sanyi sanyi na hakurin nan da ya bata, dan kuwa ko da ana azabtar da shi a hannun samarin nan da bashin giya ya haɗa su, adu'arsa daya ce a kulun, Allah ya sa ya samu ya ba marainiyar Allah hakuri kafin ya mutu, yana ta adu'ar Allah ya datar da shi da bata hakuri kafin ya koma ga mahaliccin sa, sai gashi Allah ya nuna masa , shi kam ba zai gaji da godewa wannan baiwan Allahn da ahalinsa ba, dama ya san shi farin sani, domin ya sha hanawa a dake shi idan wani abu ya hada shi rigima da wani a gidan giya, kun san gidan giya karamin yaro sai ya mare ka in ta hado ku, shi yasa yake karra tirrr da wannan rayuwa, ya je ya ga ukuba kala kala saboda yan kudaden da basu taka kara suka karya ba da kula yana kallonta ya ce" Ama ban manta fadan da nake son yi ba, waye ya baki kudaden nan masu yawa?" RAUDA ta sake sada kanta, dan kuwa ta san laifinta a sanyaye ta ce" Aba, dama Abdallah ke min ire iren kyaututtukan nan, masu yawan gaske, da su nake kashe rikicin Mama wani lokacin dan ba kulun nake iya yiwa samarin dabara su bani kudin su ba tare da sun nuna min wata hanyar ba, walahi aba ban taba wulakantar da kaina ba, ban taba ba, ko nawa zaka gani a hannuna ba haramun bane, ban taba aikata wani aikin dan na samo kuɗi ba, Allah ya kare Ni sosai daga wannan halakar " Aba ya sauke ajiyar zuciya yana yiwa Allah godiya a cikin ransa, a sanyaye kuma ya furta" Allah ya karra tsare ki, shi Abdallah din nan balaraben nan ko?, ya je wajena sau biyu" RAUDA ta gyada kanta bata ce komai ba kanta a kasa Aba ya ce" Sosai Bah din ku ya nuna min eh idan har ana iya bashi bashi da wata matsala da ta danganci mugun hali ko nasaba ko addini da za'a iya hanna masa, Ni kam na fada masa bani da damuwa in dai kina son shi Allah ya tabatar da alkhairi, shine akace to wai za'a saka nan da sati biyu, ana so kafin a maida Ni wajen neman lafiyar nan ace an daura ina nan, shin kina son shi? dan in har bakya son shi ba zan taba yarda na baki shi ba, domin ba zan so ki kuma shiga wata rayuwar kaka naka yi bayan wace kika yi a rayuwa RAUDA" kanta na kasa ne, tana jin furucin Aba tamkar wanda yake yi mata yare da yaren da ba nata ba sosai Hausar ke son yiwa zuciyarta nauyi, har ta dan dago tana kallonsa a raunane ta ce" Sati biyu kuma aba?" Aba ya zuba mata ido yana kallon yannayinta, da kula ya ce" Eh sati biyu yar gidan Aba, akoy wani abin ne? " RAUDA ta sada kanta, a hankali tana fitar da numfashi daga bakinta dan sai ta ji murar dake sandarta ta toshe mata hanci nan take "RAUDAH?" Aba ya fada a tausashe yana sake kallonta dagowa ta yi da dan sauri tana kallonsa, sannan ya amsa "akoy wani abu dake damun ki ne da ya danganci auren nan?, idan har akoy shi ki sanar min domin kina da dama tun kafin wuri ya kure maki, domin shi aure daraja gare shi, kuma maganar nan manyan mutane ke cikinta, koda ke din abar so ce a duniyar su ba zasu yarda ki saka su magana biyu ko zubar da kima a wajen mutane ba, *SHIN KINA SON ABDALLAH KO BAKYA SON SA?*" RAUDA ta yi saurin sadda kanta, a hankali ta furta" Aba ina son shi" "KINA SON SHI?" ya sake yi mata tambayar da ta fi kayar mata da gaba fiye da komai, dan bata san me yasa tambayar ke yi mata wani iri ba, ko dan iyayenta ne ke yi mata ita? Sai kawai ta sake sinne kanta ta gyada kan nata cike da jin wani rauni da kunya da kuma sake yiwa kanta tambayar menene yasa take jin wani sensation daban a kan lamarin nan? "alhamdulilah, Allah ya nuna mana, ya tabatar da alkhairi, to wai shi Abdul din karami haka yake da son dadi? kin ga Abdul harda turanceni?" Aba ya fada da yannayin barkwoncin da ya sakata yin dan murmushi, ama sam bata iya yin dariyar da abin ya dace ya sakata ba, karshe salamarta ya yi dan ya kula ta daina gane yarensa ta mike ta fito daga ɓangaren bakin da aka sauke shi ta shiga tafiya a hankali tana jin tamkar iska na son kayar da ita, bayan ita din masha ALLAH a yanke take sosai, da wahala iska ta yi mata watsawar kara in ba gagarumar iskar dake iya jijigar mota ba tanfatsetsiyar wayarta, wace tun bayan kwana uku da bacewar Tata Mah ta bata cewar yayansu ya sa aka kawo mata daga shagonsa mai sunna ONLY IPHONE dake cikin gari, wayar da ta ninka Tata a tsada da kyau, ta kampanin iphone din ce da layi harda katin da har yau ta kasa cinyewa duk irin kale kalenta a wajen su youtube ne da instagram da su tiktok bata gama cinyewa ba dan masu nauyi ne numbar ABDALLAH dake nunawa cewar shine ke kiranta ya sakata lumshe idannuwanta hawayen da suke mata zafi a ciki suka fita ta sauke ajiyar zuciya ta goge fuskarta sannan ya daga a nutse ta yi salama "Angel, ina gidanku fa, ama ban shigo baban filin wajen MALIK ba, ina daga nan wajen masu tsaro na barin dama, kin ga dare ya yi ba za'a barni shiga da mota har cen ba, Ni kuwa kirjina ke min nauyi bana jin dadin jikina yau" a hankali ta hadiye yawun dake makogwaronta sannan ta karasa wajen masu tsaron babar kofar yana jinta ta sanar masu su bar shi ya shigo, dan ya riga ya zo ba zai yiwu ta maida shi ba, gashi yace bashi da lafiya dole zata kula da shi tana nan tsayen har ya karaso aka bude masa ya shigo da motarsa sannan ta karasa ta dan dora hannayenta ta leka kanta taana kallonsa ta ce" why kake son yawon dare tsakanin hanyar nan da bata da kyau kuma baka da lafiya?" idannuwanta yake kallo yadda suka nuna alamun jika ya ce" Me zai hannani zuwa inda kike banda mutuwa? me zai hannani zuwa na ganki banda mutuwa? na zo na ga amaryana ne, wai kin san an bani ke? za'a tabatar min da ke nan da sati biyu idan ba mutuwa ce ta daukeni kafin lokacin ba?" idannuwanta da suka yi yaushi ya dora masa, a sanyaye ta furta" Abdallah, kar ka daga min hankali" murmushi ya yi yana kallonta ya ce" Kuka kika yi?" da sauri ta dan zarro ido tana kallonsa ta ce" Kuka kuma?" Kai ya gyada yana kallonta, sai ta yi murmushi ta girgiza kanta kasa kasa ta furta" Ka je gida Please, ka kular min da kanka" "Sai idan kin min alkawarin zamu yi waya!" ya fada yana turo baki, hakan ya sa ta yi yar dariya ta ce" Zamu yi waya da kai dan saurayina....." yana dariya ya girgiza kai ya ce" Allah akoy maganar da bamu gama ba, kuma ke bakya son surutu ta waya, Please ki shigo" a dole ta bude gaban motar ta shiga ta zauna tana sauraronsa yana kallonta ya ce" Dangane da maganar yarinyar da na taba yi maki a lokacin da nake maroko ne, Angel kin ga na fada maki inada matsalar haihuwa, kin san da wannan ko? shine nake tsoron zamanmu ba yara na iya saka ki a damuwa, kin amince mu daukota?" shiru Rauda ta yi tana nazari, a nutse ta dube shi ta ce" da ka ga ban nuna damuwa a kan maganar rashin haihuwarka ba, dan nima bana son na haihu, ABDALLAH bana son haihuwa saboda yadda duniya ta zama, kwarai akoy na kirki cike a duniya sai dai masu muguntar sun fi yawa, Ni idan aka barni ba zan iya rabar da kowace halitta a matsayin wace zan iya kukan jinni idan ana yi bayan mutuwa ba in aka zalunta da na yi, Abdallah, inada ciwo mai girma da aka haifar min wanda ya saka min tsoron haihuwa, ina tsoron na haihu na tafi na bari abinda na haifa ya fuskanci kwatankwacin rayuwar da na yi ko fiye da haka..............., da da hali, ka barta a hannun da zata rayu ta ji dadi, ka yi mata dukkan abinda ya dace na rayuwa ama kar ka bani" ta karashe tana sada dubanta, dan sam bata so ta yi kuka a kan wannan maganar ya jima zuciyarsa na tsintsinkewa, ya jima yana jin zafi a ransa na tashin hankalinta kuma har sai da ya ayana kalmar Allah ya saka mata a ransa, sannan ya furta" ki yi hakuri, ba haka zai hannaki neman farin ciki ba, yara sunne farin ciki, yara sunne kwonciyar hankali, idan har baka haihu ba in Allah ya sa kana da damar dauka ka rike ka dauka ka rike, Allah shi yake da komai, dan iyayenki sun rasu sun barki ba yana nufin kema zaki rasu ki bar baki da jan sawunki ba, komai na Allah ne Angel, ki yi hakuri kin ji?" kai ta gyada a hankali ta bude motar ta juyo tana kallonsa, a tausashe ta ce" ka huta lafiya" kasa amsata ya yi har ta fita ta tsaya tana kallo ya juya motar ya fice suka rufo sannan ta juyo tana ta tunanin Allah ya sa yanzu Hajia ta koma bangarenta, dan ance zasu yi zama ita da Bah da YUSUF , kuma tana matukar son yi masa godiya, walahi har a ranta take son yi masa godiya na irin yadda ya kula da lamarin uncle, kai komai ma ya dace ace ga yi godiyar sai dai bata san ta yada zata same shi ba yanzun, rabonta da shi tun a kicin din nan, bayan nan basu kuma haduwa ba, bata san lokacin shigowarsa da fitarsa ba, ama a yanzu tunda ta ga masu tsaron lafiyarsa a cen tsaitsaye ta tabata yana ciki a nutse take tafiya har ta kama kofar falon ta shiga da salama ciki ciki tana lumshe idannuwanta saboda sansanyan kanshin da ya shige mata hanci da sanyin da ya daki fuskarta da hannayenta a hankali ta ɗora idannuwanta a bayansa, saboda irin tsayuwar da ya yi hannunsa wajen kunnensa ga dukkan alamu waya yake yi kasa gaba ta yi ko baya har sai da ta ga alamun zai juyo ta dan motsa a hankali ama kuma bata karaso din ba har ya juyo yana waya din sai dai idannuwansa na sauka a kanta ya yi shiru da maganar da yake yi tamkar ana kwata a bakinsa dan ransa a mugun bace yace, domin zaman nan da aka yi dan a fada masa ne tarewa da za'a yi nan da sati biyu dole zai tare da mace matsayin tasa, da kuma bikin yarinyar nan ko me? da bikin sarautar, mace akace zai tare da ita wace zata zamo zabi ce daga Hajia, tunda da ranta dole zata zaba masa matarsa ta farko kamar yadda suke yi, da ace ta rasu ne sai mahaifiyarsa ta zaba masa kansa ya dauke gannin ta juyo ta sake zuba masa ido a karro na biyu ta ki dauke dubanta a kansa ya ci gaba da maganar har ya gama ya kashe kiran ya wurga wayar saman kujera sannan ya karasa ya zauna yana jin tamkar kansa zai fashe da ciwon kai a sanyaye ta karaso inda yake zaune, da farko ta zauna saman kujera nesa da shi kadan sai kuma ta sasabto kasa ta duka jikin kujerar a tausashe sosai ta ce" Barka da warhaka MALIK" shirun da ta ji ya sakata dagowa a hankali ta dan kalle shi, ta ga yana nan din fa, amsawar ce bai yi ba, dan haka ta sake maida kanta a tausashe ta ce" Dama ina ta so na yi godiya ne, Allah ya saka da alkhairi, na gode, na gode, mun gode , mun gode sosai Allah ya saka da alkhairi, irin yadda ka fito da Abana, ka kai shi asib......" "RAUDAH!" ya furta a cen kasan makogwaronsa, wanda ya sa ta dago da sauri saboda irin yadda amon ya ratsa dukkanin sashen jikinta idannuwansa dake lumshe ya bude a kanta, sun yi jajir ya watsa mata wani kakausan kallo, a kausashe ya ce" Ki bace min da gani!" da sauri ya sake zuba masa ido, gannin kallon da yake yi mata ya sa ta sake dubansa ta ki tashi din dan sai ta ji kaffafuwanta sun mutu murus, da tsabar tunanin me ta masa? me aka yi? katse mata tunani ya yi a lokacin da ya mike, hannayen nan nasa dake da girma irin na kakarfan maza ya dunkule ya karaso inda take hakan ya sa da sauri ta yi zaman yan bori tana rukunkume jikinta saboda mugun tsoron da ya kamata na kar aje ya daketa Rai bace ya ce" na ce ki fita daga idannuwana, ki fita a idona! ki fita a rayuwana tunda ke bakya ji, ki tashi ki bar nan!" ya idasa fada da dan karfin da ya sa Bah dake dakin Mah mikewa da sauri ya fito, Mah na binsa a baya, ita kuma a lokacin da sauri ta mike tsaye jikinta na rawa ta juya da sauri ta yi ciki kuka na kwace mata wanda da za'a saka mata wuka a wuya ta ba zata ce ga takamaiman abinda ya sakata kukan ba, idannuwan da ya biya da su ya risinar a saman lebenta ya furta" RAUDA, kar ki kawo min garaje a duniyata, RAUDA, kar ki yi abinda zan tsane ki!" Mah dake tsaye daf da Bah sunna kallonsa gabanta na faduwa da abinda suke ganni a idannuwansu ta budi baki ta ce" Azl 35 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo a tausashe sosai Mah ta ce" YUSUF?, me yake faruwa my life?" a hankali ya sake duban mahaifiyarsa da mahaifinsa dake tsaye sunna kallon sa kansa dake sarawa ya karra rikewa ga gumi yana haɗawa da kyar ya iya rintse idannuwansa ya sake budewa, yanzun ba tun karfi yake magana ba dan burinsa ya sauke abinda ke ransa sannan ya nufi dakinsa, yana kallon Mah ya ce" Yaya zaku dauko yarinyar matsayin y'ar cikinku ku kyaleta tana abubuwan nan? ita shikenan bata da lokacin kula maza ne? zance fa ta fito daga motar namiji a irin wannan lokacin, mace ce fa, shikenan ita bata da kamun kai?" hankali tashe Mah take kallonsa, Bah kuma sai ya harde hannayensa shima nasa hankalin a tashe ama kuma na Mah ya fi nasa Mah na kallonsa ta katse shi da fadin" Subahanallah, wai wace BABY?, Ni tunda nake ban taba ganninta da wani bayan Abdallah ba, ko wani ya zo wajenta bani da labari?" da mama yana kallon Mah ya ce" Shi din muharaminta ne da zai ringa zuwa yadda ya ga dama a lokacin da ya ga dama?" Mamakin Mah ya karru, ta yi gaggawar fadin" A'a fa YUSUF a'a fa, Abdallah ai ba koda yaushe yake zuwa ba, kuma yanzu da aka saka ranar auren su ai shikenan ya gama zama ɗan gida" ikon Allah kawai ya tsaya kallo kafin ya girgiza kansa ya nufi ciki da sauri ta daga kafarta da nufin binsa Bah ya rike mata hannu, da hannunsa ya mata alamun kar ta je shi ya bi bayansa Mah kam abin neman fin karfin ta ya yi, da kyar ta iya komawa ta nufi dakin su RAUDA Bah na shiga ya wuce bedroom dinsa zaune ya same shi bakin gadonsa yana rike da kofin da ya jika maganin ciwon kai, dan yana shiga ya dauka ya wurga cikin kofin ya zuba ruwa yana jira ya narke ya sha "ka tabbata, dan kawai yarinyata ta je wajen mijin da zai aureta a cikin gidan nan ne ranka ya ɓaci haka, ko kuwa bacin ran maganar Hajia ce ta shafeta, ko akoy wani abin a kasa wanda ya dace na sani tunda wuri ko zan iya magance shi?" Bah ya fada bayan ya tsaya yana kallon YUSUF YUSUF ya dago yana kallon BAH, a hankali dan yannayin da ciwon kan ya kama masa harda ido ya ce" abinda ta yanke ai na san dole zan yi biyayya, babu wani abun a kasa" Bah ya sake zuba masa ido, sai kuma ya girgiza kai a tausashe ya ce" Ko menene , ya dace ka kula, ka san me yake kaika wannan makurar,, ban saba ganninka haka ba, baka iya fushi ba Son" murmushi ya kakaro yana sake duban Bah a hankali ya furta" In sha Allah " daga nan Bah ya juya ya fice dan sam ya ki bashi damar su yi firar nan, sai dai abinda ke cen cikin zuciyarsa na neman lalata farin cikin da yake ciki na firar da suka yi da matarsa, domin tunda ya shige ya zauna yana zayane mata abinda yake faruwa ya so bata hakuri da bakin cewar ba daga shi bane hukuncin zabawa YUSUF macen aure ta fari, kuma ta kwontar da hankalinta in sha Allah ya san Hajia zata zaba masa wace ta dace, sai ta hanna shi yin wannan ta nuna masa to meye a ciki dan Hajia ta zabar masa mace, ko shi bata tunanin idan zai bijire domin fadan da suke yi ba yana nufin baya son Hajia ba, YUSUF na son Hajia fiye da tunanin bawa, dan sabanin da suke samu kuwa ba shine zai dakusar da soyayar da yake yi mata ba irin wannan halaya nata da suka karra siye zuciyarsa suka saka ya zamo baya iya daina sonta da kaunarta ne, a yanzunma ta gwada masa, shi ya san ita din mai karra ce, mai hakuri ce, mai biyayya ce, sai ga wani gagarumin abu dake iya rikita masu lissafi na neman kutso masu, ya Allah.....ka ƙaryata abinda nake zargi, domin idan har hakane ban san yaya zan iya kawar da kai ina kallo MALIK ya shiga wani halin ba, haka kuma ba zan so na yiwa y'ar mutane dole ba, ita din amana ce a wajena, abar a tausaya mata ce, itama y'a ce, tana da nata zabin kuma tana da ra'ayi, ya rab ko menene ka daidaita min cikin salama....... da wannan ya je dakin Mah ya zauna saman kujera yana jiran dawowarta BAH na nufar dakin YUSUF, MAH ta nufi na su Rauda da sauri dan yannayin da ta fice tana kuka sai da ya mugun daga mata hankali A Lokacin da Mah ke kokarin shigewa bedroom dinsu ne ta ji Muryar Salima na fadin" Me yasa duk abinda ya shafi yayanmu ke mugun daga maki hankali, wani lokacin sai in ga abin bai kai ki yi irin kukan nan ba, sai na ga kin yi kuka kamar zaki sike, shin a nan menene abin kuka haka RAUDA?, haba RAUDA ta yiwu fa kin same shi ne a lokacin da yake cikin bacin rai shi yasa abin ya sauka kanki, ba wai dan ya tsane ki ba, RAUDA yaya za'a yi ya tsane ki kuma fisabililahi?" ga mamakin Mah, duk irin abinda ke faruwa tana jira ta ji wata maganar ne daban, sai ta ji Muryar RAUDA a sanyaye sosai tana fadin" Salima, kin tabata bai tsane Ni ba?" itama Salimar sai ta gaza gane komai, kawai ta yi sororo tana kallon Raudar har ta ajiye wayarta ta mike ta nufi bayi ɗan gannin Salima ta ki bata amsa ranta sai ya ringa sosuwa, haka kawai ta ringa jin bacin rai kala kala a cikin zuciyarta da tarin jin haushin Abdallah, ko saurin me yake mata da zai sa a mata aure yanzu yanzu, ita fa auren ne kansa take gannin bata wani shirya ba, to ta barwa Abdul wa yake nufi? lallema sam baya tunani shi kam! (uhum, 🤔🤔🤔🤔1) A hankali Mah ta juya ta ki shiga dakin ta nufi dakinta jikinta a mugun sanyaye Tana shiga ta ga Bah zaune, da sauri ta karasa inda yake ta zauna daf da shi tana kamo hannayensa ta ce" Na shiga uku, ka san tare muka san su ko? Tun yaushe suka san junna? na shiga uku Bah, kar dai , kar dai, to ama kuma in har akoy wani abin tsakaninsu ai da an sani ko? ai ba zasu kyale har a saka aurenta ba ko? wayo Allahna, fushin nan na YUSUF ba banza ba, Ni kam ba banza ba!" Bah ya sauke ajiyar zuciya a nutse ya ce" na yi iya yina ya nuna min ba komai , ban san wani iri bane YUSUF, Please ki tambayi y'arki cikin hikima, idan akoy wani abin su fada mana tunda wuri dan bana son a zo a hada min tunani, a yanzu ba lalle ne na iya bari wani abin ya rikita masa lissafi ba, sai in ya fi karfina!" Mah ta dafe kai cike da zulumi, karshe dai daren nan wani iri suka kwana dan kowa da tarin tunani ya kwonta har kiraye kirayen sallar asubahi ta saka kowa ya kama gabansa dan gaisar da Ubangiji kamar yadda ta saba zuwa gaishe da Mah tun da duhu duhu kadan hakan ne yauma ta je ta duka gaban Mah ta gaisheta har zata mike Mah ta saka ta koma ta zauna, sai da Mah ta gama abinda take yi ta fuskanceta, da yannayin kula sosai ta ce" Baby, yauma zan sake yi maki tambayar da na maki sau uku a baya, dan ina son amsa ta karshe, domin hakin hakan a wuyuana yake, ki fada min, kina son ABDALLAH sosai zaki iya yin rayuwar aure da shi?" RAUDA ta lumshe idannuwanta da suka yi mata nauyi, a hankali ta gyada kanta muryarta a raunane sosai ta furta" Eh Mah " Mah ta tsura mata ido, haka kawai take ji a ranta abinda take fada ba gaskiyar abinda take son fada bane, sosai take son tambayarta da gaske ba komai tsakaninta da wanin bayan Abdallah, ama ta gaza, dan haka ta sauke ajiyar zuciya a sanyaye ta ce" Allah ya tabatar mana da alkhairi, daga yau mai gyara zata zo a fara gyara min y'ata in sha Allah, je ki huta kafin a jima zan kiraye ki mu shiga kicin mu fara girkin Larabawa" Mikewa ta yi tsaye tana jin idannuwanta sun ciko da kwallah ta juya ta fice, Mah kuwa ta rakata da kallo tamkar tace ke zo nan, karya kike ki fada min gaskiya, sai dai ta gaza dan bata san yaya zata hau yarinyar da fada ba, bata iyawa, tana kaunarta tana jin tausayinta sosai a rayuwa kasancewar coridor ne kafin a fito falo karami sannan a nufi wani corridor din a tafi dakin Salima ya sa take tafe a hankali har ta zo daf da fita daga corridor din ta ja da karfi , kirjinta na mahaukacin dokawa , a hankali ta sada kanta daga kallon tsararan rawanin dake zagaye da ni'imtaciyar fuskarsa , jikinsa dauke da manyan tufafi na dakarun sarakai, sarakai masu aji, sarakai masu ya'yan banki, suturarsu kadai abin girgiza zuciya ce bale idan Allah ya halice su da iza, da kwarjini, kallon su na hadasa danshi a ido da bugawar zuciya koda baka so ba, girmama su ya zame maka dole saboda Allah ne ya basu ba wani ba kan da ta sada yake kallo, kafin ya bi yan yatsunta dake dauke da jan lalle da kallo a hankali ya furta" Raudah......?" Gabanta ya sake faduwa, ta dago dubanta a raunane ta saka cikin nasa idannuwansa ya janye kadan daga cikin nata , kasa ya furta" Ya yi kyau" jikinta ta ji ya fara rawa, tsigar jikinta na tashi, gumi na son wanke mata fuska, da sauri ta sada kanta dan ba zata iya duban idannuwansa ba Sai dai bata tsira ba, domin dukar da kanta da ta yi ba shine ya rabata da shi ba, har sai da ta ji amon muryarsa wannan karron daf da ita ya sake furta" RAUDAH?" "innalilahi Wa inna ilaihi raj'une..." ta fada a hankali saman lebenta kirjinta na bugawa da karfi Sosai ya karanci abinda ta furta, ama bai sace masa gwuiwa ba, to shi meye kuma ya rage tace masa? wannan ai tabataciyar kalma ta maimaita dan tace daga Allah muke gareshi zamu koma, ta fa taba ce masa shedani har ta nemi tsari da shi fa ko? , a hankali ya hadiye yawun dake son busar masa da makogwaro kasa kasa ya furta" Nace ya yi kyau RAUDAH" idannuwanta dake cike da kwallah ta dago ta saka cikin nasa, da karfi ta ja numfashi ta sauke sannan ta kausasa dubanta, da karfin ikon Allah ta sakar masa zazafan harara sannan ta ja baya ta yi tsaye hadi da dukar da kanta zuciyarta na tafarfasa, bata san me yasa ba, gani take yi babu wanda ya taba wulakantata irinsa, ita a yanzun gani take yi kamar baya jin tsoron Allah, ashe shi aurema zai yi nan da sati biyu? tirrrrr tirrrrr tirrrrr da wannan hali, tirrrrr da fitinanen hali, kuma tana tausayawa matar dan kuwa ta iya ganganci, aikin banza Allah ya sa a Daura masa hudu a tashi daya kowama ya huta, itafa dama tunda ta ga idannuwansa ta gane za'a yi biye biye a nan, shi yasa ta zabi auren Balarabe dan yanzu ko bahaushe ka shige tsaf zai maka kishiya, ita kuma ba zata taba zama da kishiya ba, bata so, bafa ta so, bata so!, aikin banza wai aure zai yi , hum! ya jima a tsaye yana kallonta, kafin ya tabe baki ya yi ciki shima yana jin wani tukuki na kama masa rai, shirme kawai, karma ta yi maganar ma mana, y'ar cen gwarama a yi a mata auren nan ta tafi ko kowa ya huta, dan ta galabi kowa da kowa a gidan nan, sai rashin kunya da rashin girmama manya, aikin banza kunshin Bama wani kyau bane ya yi fa, kawai dai ya dan haska hannun ne, kuma sal ba'a yaba dan wani abin ba, shirme, dala shigowa ya yi ya ga Mah sannan ya wuce wajen wace tsohuwar su gama magana tace tana neman sa, juyar da kai RAUDA ta yi ta wuce kamar ana korarta ta nufi falo baba tana sake turo baki da maganganu a ranta da jin haushi, ta kuma yi alkawarin ita da shi ido, tunda dai haka yake! bai jima ba ya fito ya fice da jama'arsa suka nufi bangaren Hajia baba sunna zuwa suka tsaya a waje ya shige dan baya shiga wajajen nan da su yana shiga ya tarda Hajia na magana ranta bace tana fadin" Kin ga, ki tashi ki tafi ciki, ko ki koma bangaren ku, dan bana son fitina, bana son fitina, ki cire wannan tunanin a ranki, dan abu ne da ba zai yiwu ba, ba tsanarki na yi ba, ba kuma hamayanki nake zagi ba, ama ba zan taba yin haka ba, kin ga tuni an kawo min hotunan wa'inda zan zaba masa , na zai yiwu ki kawo min wannan maganar ba, tashi ki shige ciki nace!" Hajia ta fada a tsawace, hakan ya sa ta mike da sauri ta nufi cikin tana fashewa da matsanancin kuka da tarin bakin ciki hadi da alwashin da ta barwa ranta, dan bata tunanin za'a yi macen da zata zauna da YUSUF in dai tana raye! murmushi ya yi ya karasa shigowa yana salama ciki ciki ya karasa ya zauna a ransa yana ayana' Hajia Nana, na fada maki sai na galabeki, ki jira Ni!' harare hararen da yake ya sa Hajia sake tausasa muryarta ta ce" Dama ka ga hotunan da aka kawo, walahi in fada maka a nan ya'yan limami da manyan mutanen kirki ne, to ban zaba ba nace ka zaba da kanka ka ji dan arziki?" harara ya sakar mata kafin ya dauke kansa ya ce" Kiran da kika min kennan?" Hajia ta yi tsuru tana kallonsa ya girgiza kai yace" Ke dai tunda iyayena ke jin maganar ki ai kin gama da Ni, kika saka tunda asubahi ya tisoni a gaba na zo dan wannan abin? ki zaba kawai ai kin gama magana, Ni tafiya zan yi inada ayyuka " Hajia na murmushi ta ce" Allah ya huci zuciyarka, to shikenan ama dan Allah in baka so fada min mi kashe mu birne abinmu a nan ka ji? babu wanda ya isa yace ba haka ba!" mikewa ya yi yana ciro wata takarda mai dauke da check na kudi ya ajiye sannan ya dubeta ya ce" Idan basu isa ba, ki kirayeni" Daga nan ya wuce, Hajiar kuwa ta dauki kudin ta duba sannan ta yi murmushi tana furta" Ko y'ar Sarkin Saudiya ce ai sun isa a aurota, kudin nan sun isa MALIK" Tun daga wannan lokacin aka shiga hada hada na shirye shiryen biki, bikin auren mutun biyu, MALIK da amaryarsa sai kuma RAUDA da ABDALLAH ana saura sati guda a yi daurin aure aka shiga kaura sabon ginnin fadar ginnin da gaba daya Nijar harda kewaye suka dauka, domin yan zuwa gannin sabuwar fadar Sarkin garin Tsaburim sun dauki vidio da hotunna na waje waje, Bama kamar balbalin sarki wanda du abinsu babu wanda ya samu shiga cikin falon bale har ya kai ga dakunan da saura wajajen bangaren, abinda dai ake cicirawa shine an ce faloma biyar ne, wasu su ce shida , abubuwa dai gasunnan ba'a cewa komai, domin ba'a karra rikita kan mutane ba sai da aka fitar da kayan tsohuwar fada aka ringa sadaka da su, kayayyaki masu kyau da tsari, kai MALIK ya sha adu'a daga bakin talakawa domin sosai aka taimaki mutane da ayyukan yi a sabon gidan Sarki a cikin wannan tsakin, sam bai samu lokacin kansa ba, dan kuwa yana fada ne amma aikin da yake yi ba na wasa bane, dan sun bude manya manyan shagunan na furniture, su Taj na kai kawo a kan harkokin shi kuwa yana magana da mutanensa na waje , ga kuma kayan sabon gidan da ake zubawa dan kamar yadda aka yiwa kowa bangarensa sai da aka zubawa kowa abinda zai bukata na rayuwa domin ba'a far kaurowa ba sai da komai ya gama kamaluwa sannan aka kauro,ciki harda Nana domin har ita ya yi mata nata bangaren, dan ba zai taba so su yi nisa ba, ya fi so tana kusa da shi ta yadda zai idasa nufinsa a kanta! ana kaurowa shiga shiri mai sunna shiri, domin ana saura kwana uku daurin aure da bikin sarautar tuni abubuwa sun kankama ba'a kama hannun yaro a irin wannan lokacin na farin ciki zukata da yawa na cikin tashin hankali da rauni na firgicin abinda suke dannewa, tun daga kan MALIK, MAH, BAH, SALIMA, RAUDA, NANA, da y'ar NANA, sai daidaikun masu boyayar manufarsu kowa na nasa sharafin har zuwa yau da aka wayi gari y'ar gidan Nana na zubar da kumfa ta bakinta sanadiyar abinda ya yiwa zuciyarta yawa a sashen yayanta wanda ya maidata wajensa tun lokacin da aka kauro nan ya kauro bisa umarnin MALIK domin a tsakaninsu akoy kyakywar alaka ta zumunci da girmama junna, dan ko shi MALIK ya yarda da kaunar da RISLAN ke yi masa, yannayi ne ya zo da hargitsin da ba zasu mori zumuncin yadda suke so ba, gashi a yanzu gannin MALIK ya yi mugun wahala, dan tsarin Sarautar wannan bawa na tare da mugun karfin gaske ta yadda idan a da ganninsa na arha a yanzu ya zama baban aiki ko ga ma'aikatan bangarensa bale na waje, shi yasa yake samunsa a masalaci su zanta , daga nan kuma sai wata sallar dan baya rasa sallar jam'i a baban masallacin cikin fadar wanda yake iya zuwa a cikin yan sakwani dan ba nisa sosai da shashinsa hankali tashe ya nemi layin Nana ya sanar mata, sannan ya shiga neman agajin duk wanda ke iya taimaka masa, ciki harda HAJIA BABA; washhh yan yatsuna😂😂😂😂 Azl 36 *KADA A YI BA KU, BONANZA TA NOVELS DINA A KAN FARASHI MAI SAUKI, WATO 1K SU 22 CIF IN SHA ALLAH.....KU GARWAYO DAN SAMUN NAKU A BISA FARASHI MAI RAHUSA .....KU TUNTUBI NUMBARNA 93811618* *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo A lokacin da sako ya iso wajen Hajia kwarai hankalinta ya tashi, a lokacin ne kuma tana tare da Bah, wanda nasa hankalin ya fi na Hajiar tashi, domin a fitowarsa sun ci gaba da mu'amala ta yan uwantaka tsakaninsa da y'ar uwarsa sai dai ba irin na da ba, ya so kwarai ya san ba'asi ama harta Hajia sai ta nuna masa ba wani abu, shi dai abinda ya sani daya ne tsakaninta da yaronsa ya nuna mata babu wata mummunar magana kuma, dan shi ba yaro bane ba kuma munafiki bane da zai tsaya wani kwane kwane, abinda aka yi a da har shima aka dora shi sama ya yi yanzu ya gane ya daina, yana so a mutunta masa yaronsa ko a zuba masa ido, ta yiwu shi yasa zumuncin nasu ba irin na da bane, ama duda haka sunna gaisawa sosai ya rigayi Hajia karasawa bangaren na RISLAN, tuni likita ta karaso domin Hajia ta bada umarnin komai tsanani kar a fita da ita a haka a kawo likitar cikin gida ta sirri, domin a baban bangaren da suka baro aka yi tsarin madaidaiciyar asibiti aka zuba kayan bukata da kwararrun likitoci wace ke anfanin da ciki da na waje Tunda ya shigo ya zauna daf da Nana yake bata baki, domin fuskarta har ta haye , idannuwanta sun kumbure sundume kana ganninta ka san hankalinta ba a jikinta yake ba, takan kalli dakin da suke ciki sai ta ja numfashi da ajiyar zuciya, domin DAYANA itace y'arta daya kwalin kwal mace, kuma tana son abarta sosai shi yasa duk abinda zata yi take hakuri ta rungumi abarta, sai gashi DAYANA zata kashe kanta saboda namiji? kiraye kirayen sallar magariba ya saka Bah mikewa ya mata alamun zai je sallah ya dawo tare suka fita da RISLAN suka nufi masalaci bayan sun yi alwallah sun gabatar da sallar sunna hanyar dawowa bangaren na Nana Bah na gwada kiran layin matansa gaba dayansu yana ji a ransa kamar ransa na daf da bacewa sakamakon rashin ganninsu bayan da aka sanar babu wace bata ji ba, ama shiru basu zo ba RISLAN ya dukar da kansa zuciyarsa na sake neman tarwatsewa saboda irin yadda suka zamo tamkar mujiya a cikin familly din saboda halayar mahaifiyarsu, babu mai yi da su, babu mai daraja su, domin a lokacin da ta yi abin nan yadda kuka san yaɗuwar mutuwa aka abin ya yadu, kafin kace kwabo kowa ya ji kuma kowa ya sani nan da nan aka shiga tofin Allah tsine domin wannan abu da ta yi Babu abinda ya kai shi abin kunya da muzantawa, karrara ta fito ta nuna son kai a kan abinda bata da tabas, koda tana da tabas a kan ɗan dan uwanta uwa daya uba daya? hakan ya sa a yanzu dai mahaifiyarsu bata da wani abokin hulda a cikin garin nan sai masu hali irinta, ita da kanta du a takure take ga matsaloli na yau da gobe, domin ba matsalar son a dora su a mulki kadai ke yayube da rayuwarta ba, ga ta yaya ga ta wajen aiki. Bah na gama kiran daya bayan daya ransa bace yana fadin me kennan?, me yasa bai gansu ba, yana huci ya kalli RISLAN ya ce" Wai me yake damun yarinyar nan har ya kaita da shan guba? me yake damunta a rayuwa ita kuma da har ya fi karfinmu muna zaune a cikin gidan nan?" kai RISLAN ya sake sadawa yana fitar da hucin numfashi mai amon "HUMMMM." Ama ya kasa fadin komai Bah ya sake dubansa a lokacin da suka shiga dan get din bangarensu yana hangen daidaikun kuyangin da ya tabata na Hajia baba ne ya ce" Tana da wata matsala ne da ban sani ba?" RISLAN ya rasa yaya zai yi, domin irin yadda Bah ya tsaya yana nufin sai ya ji abinda yake damunta kennan? kai ya sake sadawa a nutse ya furta" Bah, shirme ne kawai ta sakawa ranta da abinda bata isa ta bawa kanta ba, da ace ta bi maganar da na fada mata ta fawalawa Allah na tabata da ta ji sauƙin abin cikin ruwan sanyi, domin tabas da Allah ya bata mafita nagartaciya, idan har abinda take yiwa din dama nata ne sai ta ga ba tare da ta daga hankalin kowa ko zubar da wata kima Tata ba Allah ya kawo hanyar da shi kadai ya isa ya kawo ta samu biyan bukata,ama sai ta ki, a kulun da irin abinda zata fito da shi, a kulun da irin fitinar da zata bilo mana da ita, shine na dawo da ita nan tunda maman rashida na nan koda yaushe tana hankalce da ita, shine yau ta yi anfani da damar nan da ta ga ta fita anguwa gidansu ta sha abinda zata bar duniyar gaba daya, ko me take tunani, ko ina karatunta? ko bata san du wanda ya kashe kansa ɗan wuta yake ba? Ni dai abin ya matukar gigita min tunani" "To ai baka sanar da ji damuwar da take sakata hakan ba, sai zagayeni kake yi da nuna min kun ishi kanku kai da mahaifiyarka ko? ba damuwa bari ita aishar ta sanar min!" ya fada ya juya ya nufi ciki dan sarai ya gane akoy abinda RISLAN ke zagayewa, sai dai ya makaro haihuwarsa ya yi ba shi ya haife shi ba bale ya zagaye shi a magana ya yi shiru ya masa biyayya!" Bah na shigowa ya tarda Hajia zaune saman kujera, Nana na zaune saman cafet hannayenta duka biyu a saman kanta tana kuka kasa kasa Hajiar kuwa na magana mai kama da fada har ga Allah bata san cewar Bah ne ya shigo ba, da ta yi shiru kamar yadda YUSUF ya nuna baya so mahaifinsa ya san abinda y'ar uwarsa ta aikata dan ya kula yanzu Bah yannayin ciwon zuciyarsa na so ya zama abu kankanima na tada shi, dan kuwa da ta ita ne da tuni ta sanar masa walahi, Bama kamar in ta ga Nana na fira da Bah normal sai abin ya ringa bata mamaki da tsoro, ta rasa a wani bigiri zata ajiye wannan halaya ta Nana, sosai take tsoron irin halin Nana, har ga Allah ko ita mahaifiyarta ta tabata idan abin son rai ne ya tasowa Nana tsaf zata zabi kanta ta barta, shi yasa itama ta yi watsi da ita take rayuwarta dan bata son mutun mai irin halin nan Hajia ta ci gaba da fadanta tana fadin" Yanzu wa gari ya waya?, kin ga tun qq duniya kema Allah ya baki mai irin halinki sak, kuma ya saka maki kaunarta a ranki, sai ki ji abinda nake ji, Nana sai ki ji abinda nake ji a raina nima, kina dai ji kina gani , baki isa ki tsawatar mata ta daina abinda kika san ba zai taba yiwuwa ba, kina kallo ba zaki iya hanna y'arki son makiyinki ba" Nana ta dago da sauri tana kallon Hajia, murya a rikice ta ce" Makiyina kuma Hajia?" Hajia ta zabga mata harara ta ce" Makiyinki mana, azaluma! makiyinki mana, yaron da tunda ya fara wasu yan rashin ji kika sako shi a gaba, a hankali kika saka mahaifinsa ke jin haushinsa, kika saka yayanku ke jin haushinsa, sannu a hankali Allah ke nuna maku shi yake da damar yi ko hannawa ama kuka kasa ganewa, ki zage shi ya ciyar da ke, kina ji kina gani da aikin naki da gadon baki yake ciyar da ke da mijinki, duk bai ishe ki ishara ba kike ci gaba da zagi nai, a gabansa a gaban iyayensa bakya jin kunya ko tsoron zuciya, kina tafka rashin mutuncinki yadda kika so, Nana kika janyo min comitin kare hakkin dan Adam Ni? dan kawai ance ba za'a dora danki sarauta ba saboda Yusuf na raye? kika zo kika kwashi kayan kunyarki duk irin yadda kika mike gaban duban al'uma kika zage shi kika ce mashayi ne, mazinaci ne ba zai yi sarauta ba aka bashi sarautar, kika ci gaba da rayuwa karkashin sa dan rashin kunya ance ku kauro kika kauro , kika ci gaba da rayuwa karkashin sa, to ta yaya Allah ba zai kama ki ba?, Allah ya bata lafiya kawai idan da rabon ta tashi ama Ni dai ba zan taba tarban YUSUF da maganar ya auri Dayana ba, sai dai ta mutu in mutuwa zata yi!" idannuwansa ya saka cikin na Nana wace ta dube shi a yannayin tsorace, hakan ya sa Hajia juyawa itama da sauri dan har ga Allah ba zata so ya jin ba dan itama jimawar nan da ya yi cikin rashin lafiya Allah kadai ya san Irin halin da zuciyarta ke ciki, komai sai ya so cakule mata, domin sai ta zama ita kadai ke kai kawo a kan lamarin rigimamenta, danma yana jin maganar mahaifiyarsa ai da sai ta yi kuka da idannuwanta na rikicewar tunani, sai Allah ya taimaketa yana jin maganar mahaifiyarsa, ita kuwa mahaifiyar tasa tana yi mata biyayya tamkar y'ar da ta haifa da cikinta, dan ita da kanta tana jinjina kawar da kai da biyayar AMEERAH, tana kuma godewa a ranta, bata taɓa nunawa bane. "Bello, kun dawo?" Hajia ta fada tana kokarin mikewa dan har yanzu bata kaza kazar da kaffafuwanta , kai tama hakura da samun kuzari irin na da ta saka a ranta ta yiwu tsufa ya sa kuzarin tafiyarsa , danma tsufa ne na mai jin dadi, dan tuni daidaikun wa'inda suke raye da suke shekaru kusan daya suka yi yarinta tare tsufan ya gama kai su kassss , dan harda wanda abin shirficewa ta same shi, ama ita da sauki sosai Karasowa Bah ya yi a hankali ya kamata ya mayar da ita saman kujerar ya zaunar da ita sosai sannan ya zauna shima daf da Hajia sannan ya sake kallon Nana yana jin irin yadda zuciyarsa ke babalewa a hankali ya furta" Haka kika yi wasa da zumuncin Allah? ashe dama irin yadda kike aibata shi dan naki ya samu shiga ne? ama Ni ai ban taba bambanta yayanmu ba, na dauki wa'inda kika haifa tamkar Ni na haifa, ashe Nine ban iya son d'a ba ko ban san zafin haihuwa ba? shine kika so ki sa na tsine masa, Ni nawa ya bi duniya ko? ashe kema kina son taki duk irin abinda yake yi? kina mancewa da irin yadda Allah ke nuna mana YUSUF mai daraja ne?, kar ki manta lokacin da kika kaini wajen wani mutun wai mai bada magani yaro ya bar rashin ji, mutumen yace ki fita yana son magana da Ni, kin san me yace? cewa ya yi daga Ni har ke sai mun ji kunya idan bamu daidaita mu'amalarmu da wanda Allah ne ke tsaye a kansa ba mutun ba, yace mu kiyaye domin shine zai ciyar da mu a gidan duniya?, duka Wadinnan abubuwan da kike ganni basu isheki ishara ba ko?, Nana kin ji kunya, kuma kin ci amanar zumunci, ama Ni a wajen Allah nake nema, kuma ko yanzu zan yi domin Allah ne, Hajia dan Allah idan har ba damuwa ki bani dama na kwatanta sanar masa ya aureta, idan har ya yarda shikenan sai a hada da ita a Daura masa biyu, na san zai yarda ne bi izinillah , ai hannunka baya taɓa rubewa ka cire ka yar, Allah shi kyauta" Daga nan ya mike ya ficewarsa a bangaren Nana wace gaba daya bata taba jin hankalinta ya yi mummunan tashi a abinda take aikatawa ba sai yau, wani tsoro da firgici ke neman rufeta, tunda take yin abin nan, duk abinda ake yi, mahaifinsa bai taba ganewa ba, kuma bata taba tunanin idan ya gane din zata wani damu ba sai yau....kasa dago da kanta ta yi har Hajia ta kara wanketa tasss ta leka dakin da Dayana ke kwonce tamkar mataciya ta fito tana fadin" Bari ki ji Nana, idan har ya ki yarda walahi babu mai yi masa dole, idan har ya kiya babu mai aura masa ita dole, domin duk balakin da kike rada masa a kanta ya kare, kin kire shi mashayi , kin kire shi mazinaci idan kin manta a gidan auren da ta kaso ta dawo aka kamata, ke kam kin shiga uku, kina da abin zagi a tare da ke kin fake kina zagin wani, sam y'arki ba matar auren YUSUF bace, ba zan so gannin haka ba , domin uwa ta gari ake zabarwa ya'ya ba kamar y'arki ba, ko kece uwar YUSUF ba zaki taba yarda a aura masa y'a kamar wannan ba, bale da irin abinda ke tsakani, Ni kam na tafi sai ki dage hakar ki ta cinma ruwa!" Azl 37 *KADA A YI BA KU, BONANZA TA NOVELS DINA A KAN FARASHI MAI SAUKI, WATO 1K SU 22 CIF IN SHA ALLAH.....KU GARWAYO DAN SAMUN NAKU A BISA FARASHI MAI RAHUSA .....KU TUNTUBI NUMBARNA 93811618* *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo a nan aka bar Nana da RISLAN , wanda ya zauna shima kansa a kasa bai iya cewa komai ba, shi kam yau ya godewa Allah da ya sa matarsa ta tafi gannin gida da yara, da yaya zai yi a gabanta ko a gaban yara irin abin nan na faruwa? ai ba mahaifiyarsa ba shima sai ta raina walahi, Allah shi kyauta Allah ya sanyaya. akace da zafi zafi akan daki dutse, tunda Bah ya je masalaci sallar isha ya ga YUSUF ya ji ai shikenan damuwarsa ta kau dan ya tabata idan YUSUF ya yarda ko mahaifiyarsa hakura zata yi, hakan ya sa bayan sun gama sallah suka fito tare, yar rakiyar da YUSUF ke yi masa sai ya nuna masa su nufi bangaren mahaifiyarsa yana son yin magana da su YUSUF bai kawo komai ransa ba, suka wuce bangaren mahaifiyar tasa, domin a yannayin ginnin da aka yi, bangare uku ke iya sadaka kai tsaye da wajen YUSUF, bangaren Bah , na Mah, sai na Hajia baba , tafiyar ba wani nisa kuma ba tsaye tsaye suka samu kansu a falon Mah A daidai lokacin da suka shigo, Mah na dakinta tana saman salaya , domin bata tashi ba, RAUDA ce kawai ke yawo da abin turaran wuta tana turara falon lungu lungu , hakan ya sa kanshin gaba daya a jikinta yake , kuma tana jin dadin hakan dan haka take bi hankali kwonce tana turarawa har ta ji salamar Bah wanda dama yakan shigo fiye da uku a wuni koda ba girkin Mah bane, sun saba sosai da ganninsa a bangarensu, YUSUF Ne rabonta da shi ido cikin ido tun da zasu kauro da ya tuko su a mota shi da kansa, ita da Mah da Abdul , shikenan bata kuma ganninsa Da murmushi ta juyo tana amsa salamar Bah , sai dai a hankali murmushin ya bace a fuskarta saboda wanda ta gani tare da Bah din ya karasa saman kujera ya zauna ba tare da ko kallonta ya yi ba Bah ya ce" baby kirawo min mamanki" Ajiyewa Rauda ta yi tana amsawa ta nufi dakin Mah, shi kuwa YUSUF harda tatare girarsa yana kallon BAH ama kuma ya kasa yi masa magana dan ba zai ce masa komai ba gaskiya, ya yi , su suka sani idan sunna so su dasa mata barima du su suka gano, ƙatuwar budurwar da d'anta gayanan shima katon saurayi ama a rika wani ce mata baby? tana sanarwa Mah ta fito ta nufi kicin dan dauko masu dan abin motsa baki, Mah kuwa ta fito ta karaso falon tana murmushi ta ce" Da uba da d'ansa Allah ya sa ta samu ne aka zo a gutsura min" Bah ya yi murmushi yana nuna mata daf da shi ta zo ta zauna tana kallon RAUDA ta kawo kayan sha ta ajiye ta nufi dakin Mah din ta yi zaune ta shiga kunce kanta da Mah ta yi mata manyan kitso kuma tace ta kunce dan tun gobe wai za'a yi mata kitso da kunshi,....uhum, idan ta tuna jibi jibin nan ne daurin aurenta sai ta ga abin kamar a mafarki A tausashe Bay bayan sun yi yar rahar da suka saba ya gabatarwa da su Mah abinda ke tafe da shi Mah ta jima tana kallonsa kafin ta sauke Gwauron numfashi ta dauke dubanta a kansa a nutse ta furta" KA yi hakuri Aban YUSUF, Ni kam ba da yawuna ba, ba zan lamunta ba, a Daura masa wace Hajiar ta zaba masa kawai, idan ya so in yana ra'ayi zai zabi wata da kansa daga baya" Ido Bah ya zuba mata, kallo irin na bai zaci koyarwar daga ita za'a samu ba, dan haka ya gyara zamansa a tausashe ya ce" Ki yi hakuri maman YUSUF, na san abu ne dake iya yi maki wahalar amincewa, ama ki yi hakuri, domin Allah zamu yi, kuma mu dubi lafiyar yarinyar ba dan mahaifiyarta ba, kin ji?" Mah ta dago idannuwanta da suka fara cenza launin kala ta zuba masa tar cikin nasa ta ce" Zai fi kyau mu bar maganar nan " dubansa ya kai kan YUSUF wanda ke zaune idannuwansa a kansu, dan a waje daya suke zaune, shine a facing din su gannin bai ce komai ba ya sa ya sake dubanta ya ce" Ba zan iya bari ba, ai inada damar zaba masa matar aure ko? to na zaba masa Dayana!" Mah ta yi murmushi mai ciwo ta gyara zamanta da kyau tana kallonsa ta ce" Eh kana da dama, ta farko ma ai damarka ce, ama ka sani abinda ya sa da na fada maka yadda na yi da yan uwana a kan maganar ƴaƴansu kace kwarai na yi daidai haka zai faru da taka yar uwar, Yaushema , Yaushema YUSUF ya fita daga mashayi mazinaci daga bakin ku ku duka?" ido ya zarro yana kallonta da sauri ya furta" AMEERAH!" Mah ta mike dan ta kula bayan shashasha da aka dauketa ana so a nuna mata mahaukaciya ce ita, rai bace ta ce" ABAN YUSUF, nace bana so, na ce ba za'a min ba, a bar min dan iskan da ake zagi hakanan ya samo daidai da shi, ko ta farkon da na amince ka san na yi karra ne saboda UWA!, bayan wannan babu wata karar da zan yi kuma, Nana ta nemawz y'arta magani sannan ta bata miji kamilale, ama ba YUSUF ba!" daga nan Mah ta wuce dakinta kirjinta na sama sama, numfashinta yi mata wuyar fita, dan nan da nan ta ji tamkar athmarta zata tashi A birkice Bah ya dubi YUSUF ya ce" Kana kallo tana son daga min hankali ta dagawa kanta a kan wannan abin da ba zai wani rageta da komai ba?, kana kallo sai abubuwa take koya wai Nine zata ce ba za'a yi ba? " YUSUF ya sada dubansa, dan ko ba komai mahaifinsa a yanzu bashi da abokin shawara sama da shi, tunda ya daina zaginsa kuwa shima yake gudun zuciyarsa a tausashe ya furta" In sha Allah, ba zata tada hankalinta ba, ka yi hakuri, ka bata lokaci amma kar kace tashi daya zaka sakata dole, kar ka manta irin abubuwan da suka ringa shiga tsakaninsu" A dole Bah ya yi shiru , ya kasa cewa uffan, karshema ya fice a falon dan zuciyarsa dake ta dokawa da irin yadda ta fice daga wajensu Sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya mike ya nufi dakin na Mah A hankali ya bude ya shiga, idannuwansa suka sauka a kanta saman mamakeken gadonta, kanta saman cinyar RAUDA hannayen RAUDA din rike da hannunta idannuwanta lumshe ko barci ya dauketa? Allah masani, shi dai tunda suka yi ido hudu da RAUDAR ya yi tsaye har sai da ta dauke dubanta sannan ya karaso a hankali ya duka ya kawo hannunsa a nutse ya janye na RAUDA wanda hakan sai da ya sa suka kalli junna da sauri RAUDA ta dauke idannuwanta kirjinta na rawa, shi kuwa a hankali ya rike hannun Mah kasa kasa ya ce" Mah, kin yi barci?" idannuwanta ta bude da suka dan fara cenza kala ta dube shi a tausashe ya furta" Kar ki daga hankalinki, a kan abinda kike da damar cewa a yi ko kar a yi, bakya so ko?" Mah ta gyada kanta a hankali tana sake kallonsa Murmushi ya yi ya ce" Ba zan yi ba" Mah ta sake dubansa ido cikin ido, ya sake tabatar mata cewar ba zai yi ba, dan haka ta ringa sauke ajiyar zuciya, ama cen kasan zuciyarta cike da mamakin mijinta take, ohk shi mai yar uwa ko? ita ta ki nata saboda ba zata taba iya amincewa da wannan soyayar ta rana tsaka ba shine shi zai amince da nasa? ba zata hanna shi zumunci da Nana ba, yar uwarsa ce , ama ba zata taba amincewa da wannan abin ba! never! Ya dan jima har sai da ya ga ta fara barci , RAUDA ta sauke kanta saman gadon a hankali ya mike ya dora kaffafuwanta sosai ya gyara mata kwonciya sannan ya dago ya juyo, nan suka sake yin ido hudu da Rauda Wace ta yi saurin sada kanta, shima ya samu damar kare mata kallo kafin ya girgiza kansa ya fice a dakin cike da takaicinta, abu daya ya sani idan har ta yarda ta yi masa gangancin da suke shirin yi jibi ba zai taba yafe mata ba! ba zai taba yafe mata ba! ................................................. washe gari tunda safe gidan ya ringa cika da baki, jama'a ta ko'ina suna zuwa ana ta shirye shiryen auren MALIK A cikin part din Mah yan uwanta da mutanenta na arziki ta ko'ina sunne ke kai kawo ana ta hulda irin ta manya karfe goma na yi Mah ta tashi RAUDA ta saka ta yi wanka wannan ta rakata dakin da ta ware saboda harkar kitson ta da kunshinta, karfe goma da yan mintunna Bara'atu ta karaso gidan da akwatinta domin ta yi iya yinta mijinta ya amince mata ta kwana dan ta fita daga girki yau ita da amsar girki kuma sai ya yi kwana biyu a dakin dayar matar, hakan ya sa hankali kwonce da kansa ya kawo ta yana fada mata zasu hade ne gobe ai saboda daurin auren SIR. Tunda ta karaso Salima ta samu ta fice dan idasa shirye shiryen kayan RAUDA din, domin harkar kayan lefenta kiri kiri Mah ta nuna ba za'a kawo ba a zuba a dankareren gidan da zata zauna wanda ABDALLAH ya tanfatsa , ta nuna akoy sutura da za'a yi mata a nan , wadinncen yan kai amarya sa karba, ita kuwa ta yi masa haka ne dan sarai ta san bashi da kowa a garin sai irin yan cin arzikin nan, ba zata so a cakula mata lamarin y'a ba, in sha Allah idan an kaita gobe ta tarda kayanta kawai ya kai ajiye, Mah din kuwa tuni ya je ta ga kayan da ita da Salima da gidan da komai, harda dankareriyar motar da aka siya mata a kampanin YUSUF a parker as gift na oyoyo tunda Atu ta zo take hankalce da yannayin RAUDA , gaba daya kana ganninta zaka gane tunaninta a rarrabe yake, duk irin yadda ta yi dan ta kawo hankalinta kanta gudun kar ta gane halin da take ciki sai da ta ringa tambayarta lafiyarta? me yake damunta? bale zuwa yamma da aka shiga shirye shiryen sakata a lalle kamar yadda tadar garinmu yake idan amarya budurwa ce ana sakata a lalle du sai ta idasa rikicewa ya zamo bata magana bata amsawa har sai da Atu ta sanarwa Mah dake cen cikin baki sai walwali take domin tun daga kan shigarta har fara'ar dake fuskarta zaka gane tana cikin wani hali na farin ciki ne ko da Mah ta shigo ta sameta an gama wanke kunshin ya yi wani irin kyau ta zauna daf da ita dan mai kunshin ta gama shafa mata turare a tausashe ta kamo hannunta ta ce" Baby, ko dai rikicewar za'a barni ne? to ba gari guda muke ba? idan kina so du safia sai in je in ga yaya kika kwana dan Ni kam har sai an ringa yi da Ni ana cewa wata irin uwa mai zuwa gidan y'arta" daria mai kumshin da Atu ke yi, Atu na kallonta tana karantarta, kai, ta kasa yarda cewar babu wani abu dake damun RAUDA, ta san RAUDA tun sunna yara, ko da ido ta yi magana zata iya fassara abinda ta ce, sam ta kasa samun sukunin yannayinta , wani abu na damunta, wani abu mai girman gaske, ama kuma ta ki fada, a haka har aka gama shirya sakata a lalle domin gabanin sallar magariba ake sakawar, Tunda aka fitar da ita baban falo dan saka lalle aka zaunar da ita saman cafet aka cire mata hijabi Sarkin kida ya fara kidan nan mai hawa kai, zabiya nata , makeriya na nata, masu daukan vidio na dauka, masu hawaye na hawaye hankalinta ya idasa tashi a hankali ta kankame Atu aka shiga shafa mata lalle , kanta, hannayenta,kirjinta dai da sauransu ana darzarta har aka gama aka lulubeta luf sannan aka mikar da ita Mah da Atu suka kaita dakin Mah suka nufi bayi da ita dan yin alwallah ta gabatar da Sallah kafin cin abinci a irin lokacin ne kuma RAUDA ta dauki wayarta tana ta amsa kiran Abdallah tana tsokanarsa shima yana ramawa har ya shaida mata abinda yana fadar, kuma a nan zai kwana? ita dai ta ki bashi RAUDA har ta gama sallah ta kwonta ta ki sauraronta, dan ba yadda bata yi da ita kan su yi fira ko zata iya yi mata magana amma fir ta kiya har sai da itama lokacin nata barcin ya yi ta hakura ta kwonta zuciyarta cike da tunanin abinda ke damun aminiyarta karfe uku na dare message ya shigo wayarta kasancewar ba barcin ta samu ba sai ta laluba ta duba message din na dauke da kalamai ne kamar haka "kin san bakya son sa, me yasa kika cika kafiya ne?" haka kawai take bin message din da kallo, wani bakin ciki na turnuko mata zuciya, ta ki ta amsa dan a tafiyar nan ta fi so ace ta tafi ba tare da ta nuna ta gane Yaren mai Yaren ba "ki sani, idan kika yi haka, kin kuntata min, kuma ba zan taba yafe maki ba! RAUDAH tunda na fara gannin ki, na san na hadu da *AZAL DINA!*" Yanzun kam zaunawa ta yi zuciyarta na kunna ta shiga rubutu kamar haka" kai ne *AZAL DINA* domin kafin ka ban san ciwon nan ba, kai ne AZAL DINA saboda kai ke son hadasa min fitina a duniyata, kana tunanin Ni mai iya raba makiyi ce bale wanda ya zamo tsokana? IDAN KA YARDA KA AURETA SAI NA DAME KU, WALAHI SAI NA DAME KA!" daga nan ta tura sakon a hankali ta kwonta zuciyarta na tabatar mata da lalle wanda take tunani ne,...to ama ita da kanta bata san me ma'anar furucinta ba, abinda ta sani daya ne ba zata taba iya yafe masa idan ya auri wata ba (tambayeta itace, da kuke cin alwashin nan, shin akoy episode din da muka rasa wace kuka furtawa junna kalmar so?....🤔🤔🤔🤔) babar rana Rana bata karya ................lokaci na zuwa sai dai mai rai ya mace ... ........ a yau take babbar rana, 😌😌😌😌😌😌😌😌🥺🥺🥺🥺🥺 Azl 38 *KADA A YI BA KU, BONANZA TA NOVELS DINA A KAN FARASHI MAI SAUKI, WATO 1K SU 22 CIF IN SHA ALLAH.....KU GARWAYO DAN SAMUN NAKU A BISA FARASHI MAI RAHUSA .....KU TUNTUBI NUMBARNA 93811618* *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo Ranar da ta zamo baba a wannan ahalin ta farin ciki bana tunanin ta zamo ta farin cikin ga fani biyu, domin tunda aka wayi gari Mah ke kan RAUDA, har likita ta zo ta dubata an yi mata allura saboda zafin da jikinta ke dauke da shi, gata gum ta ki ta kula kowa, karshema Mah din ce da kanta ta kaita bayi duk irin yadda take nokewa ta kasa kiyawa Mah ta taimaka mata ta gasa mata jiki sosai suka fito daga ita sai Mah sai ATU dake Binta da kallo Mah ta saka Atu ta dauko wasu kayan, domin yannayin nan nata ya zama dole a kyaleta da cenje cenjen kayan da aka so a wuni ana sakata yi da mak'up, dan kuwa koda an tirsasata an yi kwaliyar ba zata yi kyau ba, karshe ana gama turareta da turaran wuta ta nade saman gado idannuwanta a rintse kanta na sarawa hannunta daya na cikin na Atu ta jimke sosai ta yadda Atun ke karra karantarta Da kula Mah ta ce" Daughter dan Allah ki kular min da ita, zan rufe kofar nan da ky zan ringa kawo maku abinci da kaina idan ke kina son fita sai ki sanar min na kawo maki ky, dan in dai na bari a bude dole sai an cika mata dakin an dameta , ga wayarta nan akoy numbana idan wani abin ya taso ki kiraye ni Please" Atu ta amsa Mah da girmamawa tana kallo Mah ya sake kama hanyar RAUDA ta dago da dubanta a nutse ta ce" baby , ina zuwa kin ji, yan daurin aure tuni sun taru, bari na je na dawo"" RAUDA ta gyada kanta tana lumshe idannuwanta, Mah ta juya ta fice ita kuwa a hankali ta silale ta dora kanta a saman cinyar Atu wace itama tana ji tana gani ta kasa shiryawar dan yannayin RAUDA ya gama rikita mata lissafi, ta rasa inda zata kama, kai ko bakin da ta tabata yau zata ringa yi ta ko'ina bata san yaya zata kula da su ba, dan bata san ta inda zata iya barinta a wannan yannayin ba, kuma tsaf ta ki yarda da abinda Mah ke son nunawa, wai tsoro ne irin na kowace budurwa na ranar aure ya sa RAUDA shiga wannan halin, kai, ta rasa me yasa ta kasa yarda da hakan, kwarai ta san da zata iya shiga wani hali ama ba wai na tsoron wannan ba, ta fi kyautata zaton tuna marigaya ne ya sakata a wannan halin shi yasa ta kasa katabus ita dinma A dayan bangaren kuwa, a cen cikin dakinsa na biyu, zaune yake bakin a bakin kujera, hannunsa rike da cofee mai dacin gaske yana dan surba yannayin hankalinsa kamar ba a cikin duniyarmu ta mutane yake ba, idannuwansa sun yi Jajajir, jijiyoyin jikinsa sun yi birde birde tun daga na hannayensa har zuwa na kansa sun yi wani iri tamkar wanda yake cikin matsanancin halin rashin lafiya Tun zuwan Bah na biyu dan ya sheda masa tawagar SHAHEED sun karaso an tafi yiwa su NAJEEBA rakiya bangaren Mah yake so ya dan motsa dan ya karasa baban falonsa, ama ya kasa daga koda ƙafarsa daya ce bale ya nada rawanin dake ajiye daf da shi wanda Bah ya zabar masa , yana nan zaune Bah ya shigo, ya sha shiga wace sai dai mu ce masha ALLAH domin ya dauki manyan kaya sai walwali yake tamkar shine ango, bakin nan nasa kuwa hakoransa a waje ya kasa hanna kansa sakin murmushi na farin ciki ga hularsa ta kafu a saman kansa ya zo inda YUSUF ke zaune da dan yannayin mamakin gannin a nan din dai yake a zaune? gashi bai ajiye cofee din da yake sha ba har yanzu? Sai ya ji kamar hankalinsa zai tashi yana mai tabatarwa kansa bashi da lafiya ne, da kula sosai ya zauna yana fadin " Son, ko baka da lafiya ne?, SHAHEED na baban falo, bayanshi duk wasu bakin dake daf da kai sun karaso tuni fa, ko na zaka iya halartar taron bane?" Idannuwansa ya fara kiftawa masu nuni da yana raye dan bayansu babu abinda ke nunawa, ya kai dubansa kan mahaifinsa a nutse ya mikawa Bah cofee din ya lumshe idannuwansa ya gyara zamansa yana kallon BAH tare da bashi rawanin ya yi kokarin sakar masa murmushin da bakinsa labansa sannan yana yi ya gimtse yana kallon BAH wanda ya kasa gane abinda ke damunsa, sai dai gannin ya bashi rawanin hakan na nufin yana iya zuwa, sai kawai ya shiga yi masa nadi, nadi na gani na fada, domin Bah dama kwararre ne a fannin nadin rawani yana gama masa ya sakar masa murmushi ya furta" Masha ALLAH, Allah ya tsare KA MALIK, tashi mu je" mikewa ya yi yana jin turaran da aka makawa suturarsa har kamar ya yi yawa, domin tun karfe hudu Mah ta zo ta yi ta yi masa addu'a sannan ta fitar da kayan da zai saka ta yi ta turare su , sai da Hajia ta iso ne ta tafi , ita kuma Hajia da ta zo ta ringa masa hade hade abubuwa masu daci tana bashi sannan ta saka masa turaren wuta da hayaki a daki, shi dai yana biye da su da ido sai da ta tafi ne ya cire jamabiyar da ya yi sallah da ita ya nufi wanka dan kaurin abin nan ji ringa yi ya karra dagula masa lissafi. A nutse ya fito baban falonsa idannuwansa na sauka a fuskar SHAHEED, Bah kuwa ya fice dan sanar da su fitowarsu kallon ido cikin ido suka yiwa junna YUSUF ya janye nasa yana karasawa inda yake zaune yana gannin YUSUF ya karaso ya mike tsaye, suka kama hannun junna sannan suka yi gaisuwar nan da aminai ke yi ta hanyar dukan kafadar junna kadan haka sannan ya dube shi ya ce" Man, jikinka zafi, Are U ok?" YUSUF ya dan kai hannunsa wajen hancinsa a hankali ya dan shafa, sannan ya masa alamun lafiya, kana suka fara tafiya, sai dai duk irin yadda ya kasance mutun mai surutu a gabansa a yau din bakinsa gum yake , har suka fito wajen ya karade da hayaniya da busa ta mamaki, ga kade kade irin namu na gida da ake yiwa sarakai kai ko kai ba dan gidan sarakai bane sai tsigar jikinka ta ringa tashi saboda abin baba ne, na manya ne tunda suka zauna wajen daurin auren nan ya kasance zuciyarsa na karra cinkushewa bai yarda da cewar eh lalle ta faru ta kare ba sai da aka daura nasa auren da amaryarsa , yarinya yar dangi gaba da baya, wace ko a garin ana maganar ahalinta domin sun yi fice sosai da arzikin da kuma kyau da isa, yarinya mai sunna AMNAH , a hankali kunnayensa suka ringa jiyo masa shelar daurin aurenta, idannuwansa dake lumshe ya dago ya sauke a kan ABDALLAH, wanda fuskarsa ta cika da yalwatacen murmushi a hankali ya dauke dubansa ya kai fuskar SHAHEED dake kallonsa sai kuma ya dauke ya ci gaba da kallo har aka daura aka gama , aka shiga shelawa ana ta taya junna murna kansa bai sara masa da mugun karfi ba sai da aka sanar da Tabatuwar daurin auren a lasifika mai karfin amo, a nan ya idasa lumshe idannuwansa a hakimce a saman kujerarsa ta mulki ta dakin daurin aure .....a irin lokacin ne kuma ko'ina ya dauka lungu da lungu, sako da sako na baban gida, inda babar jakadiyar bangaren Mah ta shigo falon ta rangada guda mai kaifin tsiya muryarta sama sama dan zata so ace itace ta samu goron kawo albishir ta shiga sanar da daurin auren yan gata ya tabata, muryarta a bayane take fadin boyayiyar amaryar uban talakawa da kuma mijin autar Mah, a irin lokacin ne Salima dake sanye cikin mahaukaciyar shadarta tana dauke da faranti mai dauke da kayan lambu na Rauda Ta bude dakin da RAUDA ke ciki , Muryar jakadiyar ta kai kunnayensu ita da ATU A lokacin da basu ankara ba , basu kawowa ransu ba suka ga RAUDA ta mike tsaye tana zarro ido, sai kuma ta dora hannayenta bibiyu saman kanta ta fashe da matsanancin kukan dake tukarta ta zube jikin ATU muryarta na furta kalma kamar haka" Shikenan , ba cuci kaina, shikenan na zabi taurin zuciya na halaka kaina, shikenan an min katanga da abinda nake tunanin babu katangar da zata iya shiga tsakaninmu, innalilahi wa inna ilaihi raj'une!" A rikice Atu, da Salima da ta idasa shigowa ta ajiye abin nan suke kokarin tayar da ita , suke kokarin ganin ta tsagaita ta saurare su, ama ba hali, ta ki ta saurare su, ta ki ta tsagaita kukanta, wanda kana ganni zaka gane idan ta ci gaba da yinsa a haka komai na iya faruwa da ita sakinta Atu ta yi ta karasa ta dauki wayarta, jikinta na rawa ta shiga call ta ringa bincikawa, sai dai duk abinda ta so ganni bata gani ba, domin furucin RAUDA ya sakata wani tunanin da ya kayar mata da gaba har zata ajiye mata wayarta a kirawo Mah, sai ta daina ta shiga message kai tsaye idannuwanta na sauka a saman numbobin nan da idan ka gansu tabas ba numbobin kannanun mutane bane, domin su dama numbobin manya sun kasance sunna kamanceceniya da junnansu , sai ta yi tunanin ko numbar Abdallah ce, ta so ta fita ama gannin message uku ne kawai a ciki sai ta shiga kai tsaye ta shiga karanta message din tana karantawa jikinta na rawa, idannuwanta na yin waje da sauri ta dawo wajen da Salima ke rungume da RAUDA rai bace ta ce" Ke Salima, saketa, saketa, ke waye wannan?, numbar waye wannan nace?" gaban Rauda sai da ya kwonci kwonci ya fadi, lokaci daya kukanta ya dauke, ta yi dif, wanda hakan ya saka Salima dake share nata hawayen gaggawar neman dagota ama ta kasa dan ta riketa taf kamar wace ke tsoron yin ido hudu da ATU "No, no, no, ba zaki tarka ba, ba zaki taba tarkar aikata abinda nake tunani ba, domin ban ga abinda zai saka ki aikata haka din a yanzu ba, waye nace wannan da yake tuna maki bakya son Abdullah? RAUDA wani kike so daban shine kika auri Abdallah? aure! RAUDA kin san menene aure kuwa? menene dalilin da zai saka ki aure shi ki halaka kanki a banza a wofi? an gaya maki shi idan baya son ki zai aure ki ne?, rayuwar aure fa ba rayuwar wuni guda bace wace za'a ce ka je kawai wuni daya ne ka jure , a kan me kika yarda kika....." "Dan Allah ki rage muryarki, kar ki yi Mah ta ji, dan wanda kike tambaya ta ko wanene nima ban san ko wanda nake tunanin bane, haukana ke sakani tunanin shi ne, saboda abubuwan da suka hada Ni da shi, kuma walahi walahi Ni dai a yanzu Ban san shi din bane wanda kike tambayata a kai ba, ina zargin haka din ne kawai, kar ki yi Mah ta ji ki!" RAUDA ta fada muryarta a raunane, tana langwabar da kai dan ta ga ATU zata zuba mata hauka, bayan ita dai ta san eh lalle abinda ke cikin zuciyarta mai karfi ne da take tunanin an wulakanta mata zuciya, ama bata san takamaiman abinda take yiwa din in shine wanda ya yi mata msg ko ba shi bane Salima da ta yi mutuwar Zaune tana kallon su cike da rashin fahimta ce ta taso da sauri ta amshi message din ko zata gane abinda suke yiwa din? a lokacin da ta diro ta karbi wayar ta karanta numbar dake kai, kanta ya mahaukacin daurewa zata karanta sakon da numbar ta kunsa RAUDA ta saka ihu, har tana manta cewar wai bata da lafiya ne, ta diro a haukace ta warce wayar, daidai lokacin da Salima ta budi baki ta fara magana daidai lokacin ne kuma aka turo dakin aka shigo, SALIMA kuwa na fadin" WANNAN DIN, AI NUMBAR MALIK CE, NUMBAR BAH KARAMI CE, ME YAKE FARUWA NE?" 🥹🥹🥹🥹🥹🥹🥹🙄🙄 Gandar rubutu ta kama mar'atusaliha a zo a yiwa mar'atusaliha solidarity a ringa karbar BONANZA ta LITATAFAINA SU 22 CIF a farashi mai RAHUSA 1k, 1k 1k 93811618 ne numbana Sarai furucinta ya sauka a kunnen Mah, sai dai ba zata iya tantance abinda yake faruwa ba a lokacin da ta shigo dakin ta gansu a tsaitsaye tamkar zakarun dake fada A tausashe Mah ta ceX Lafiya? ko jikin na baby ne?" RAUDA ce ta yi gaggawar ba Mah amsa cewar" Ba komai Mah, fira ne muke yi" hakan ya sa sauran kallonta, har Mah ta idasa shigowa tana fadin" To alhamdulilah haka nake son ganninki, ku yi zaman ku wajen nan Bama zai zaunu ba, zuwa yamma za'a kai ki wajen Hajia baba in sha Allah kafin a kaiki dakin ki, Atu kina da baki ne?" Bara'atu ta ja numfashi a hankali ta ce" Eh Mah, mahaifiyata da daidaikun mutane zasu zo ama idan sun zo din zan zo na kai su wajenki su zauna saboda nan din ba zai yiwu ba" Mah ta karasa ta dauki abinda zata dauka ta fice tana fita Salima ta je da gudu ta saka ky a dakin sannan ta dawo tana kallon RAUDA ta ce" Bani msg din na karanta, menene a cikin msg din? me yake damunki ne? yaya aka yi na ga numbar ta yayanmu ce? numbarsa ce, pvt numbarsa, nima na hadaceta ne saboda yawan kiran Mah da yake yi da numbar " RAUDA ta jimke wayarta ta kai zaune saman kujera tana hankalce da su Atu ta ja wani irin tsaki ta zauna tana dafe gaban goshinta, a kufule ta ce" ki warware min abinda yake damuna tun kafin na hargitsawa kowa tunani a gidan nan RAUDA" RAUDA ta sake hade fuska ta ce" Ke wai me kike so na fada maki ne?, abinda kike tunanin ba haka bane, kuma Ni na bada amsa ne a cikin lalube" Jikin Bara'atu ya karra yin sanyi, Salima kuwa ta idasa shigewa a cikin duhu, dan gaba daya ta rasa inda tunaninta zai sauka a irin wannan lokacin Shiru Bara'atu ta yi mata, ita kuwa ta yi tsuru tsuru, wayar nan a damke a hannunta, ciwon dake zuciyarta sai ta dane shi ta hanna shi kuma fitowa domin ba zata taba yarda wani nasa ya san abin nan ba, ba zata yarda ba sam! Salima ta jima tare da su, a dole ta sake tafiya saboda baki ne da ita sosai kuma sunna ta kiran wayarta Tana Fita Atu ta sake tado zancen tana kallonta cikin ido ta ce" Ki dan bani haske, RAUDA me hakan yake nufi? soyaya kuke yi da shi?" RAUDA ta girgiza kanta a hankali, sannan ta sake dago idannuwanta ta zuba mata su a raunane sosai ta ce" Kina tune da ranar da na ki zuwa makaranta safe da yama, har washe gari kila zo gida tunda sassafe kika ga ko Lafiyana?" Atu ta daga mata kai, dan a lokacin sai da RAUDA ta yi kwana uku cif bata fita ba RAUDA ta yi murmushi tana girgiza kanta ta ce" A ranar da na fita da wani saurayina da dare yace zamu je mu siyo abinci, da muka je siyan abincin ashe da aka zuba nawa an zuba magani...., kuma ban san yaya aka yi ba dai shi ya gani, ban sanshi ba, ban taba haduwa da shi ba ama ya biyo bayan saurayin nawa har mota sai da ya shiga ya fido shi ya tambaye shi abincin dayan na waye?, shi kuwa irin da abin garajen nan yace bai sani ba waye shi? ya sake tambayarsa a kausashe , ke dai in kare maki zance a ranar da ya ce min sai in gyara zama dan an zuba magani a abincina, Ni shi nake kallo, jin furucin nan na fito hankali tashe na so yiwa saurayin nan nawa rashin kunya shima ya so ya nuna min sakaran halin namijin dake fada da mata, Atu ban shirya ba ya daukeni cimak ya maida bayansa ya ci uwar saurayin nan, da kyar aka raba su, sannan ya rufeni da fada harda kashedin ya gane fuskata na yarda ya kuma gannina da wani dan iskan zan fada...." Ta yi murmushi ta ci gaba da fadin" Babu wata alaƙa da ta shiga tsakaninmu ta wani alamu, tun daga ranar ban kuma ganninsa Bama sai ranar aurenki, sarai na gane shi, sai dai irin yadda yake ta hade rai da furucinsa kamar mun zo neman wani abu sai na share shi na dauke kaina, ko da muka kai ki mun hadu da shi a hanya ina dawowa, sai kuma ranar da na je restaurant na ganshi , kuma a ranar ne muka yi adaidaita daya muka yi accident. ......, a kaf maganar nan da nake yi maki maganar da ta hadani da shi bata fi sau hudu ba, na farkon nan da ya min, na biyu a cikin adaidaita da ya nemi na bari a kai shi wajen Mah, na uku fadan da ya min dan na fita da dare wajen ABDALLAH, sai ranar da yace kunshina ya yi kyau!" Ta karashe tana dantse lebenta, Atu kuwa zuwa lokacin kirjinta har sama sama yake yi saboda yarin tashin hankalin da take gannin RAUDA ta gama sakata Murya da gagawa ta ce" Kina nufin, da gaske MALIK din ne ko dai ba shi ba?" RAUDA ya kalli yannayinta, kamar firar na neman rikita mata lissafi, kamar kuma wace take iya kai mata naushi, dan haka ta sake gyara zamanta tana kallonta ta ce" Shine mana, ke sunansa YUSUF ne" "Innalilahi Wa ina ilaihi raj'une!" Atu ta fada da karfi har sai da RAUDA ta zabura ta mike tana duba bayanta domin yadda ta yin walahi ta zata wani abu ta ganni a bayanta Rai bace Atu ta ce" Ke zauna dan ubanki! zauna nace, yanzu Ni kika yiwa wannan danyen aikin? Ni kika watsa haka? innalilahi yanzu jira kike yi bayan yaba maki kunshi da ya yi ya ce wance ina son ki? an gaya maki manyan nan haka suke? RAUDA Sarki ne fa, kuma tun kafin nadin sarautarsa mahaukacin mai kudi ne, wanda yake tafe ko a cikin abokansa cikin izarsa, ke kin ji in Alhaji na maganarsa irin yadda yake fadi? shine kike jira yace maki me bayan abinda ya nuna maki a aikace?" RAUDA ta ja tsaki , zuciyarta na tafasa tana jin kai ita fa sarai tana iya murje komaima ta yi kamar bata taɓa Sanni ba a kan shirme, itama a dan zazafen ta ce" Sarki? sarki kika ce? ohk...., ya yi, ya je ya yiwa wasu sarautar ba Ni ba, ke kina so , so kike ki ce min, saboda tsabar balaki da wulakantar da kai, Ni mace nice zan hankalta da ana so na har na lalata auren wanda ke son nawa fisabililahi na zabe shi? Allah ya kiyaye, walahi ba zan taba yarda da wannan abin ba! ke bari ki ji, koda abinda kike tunanin haka ne wato yana so na, na ƙaryata, dan kuwa so din in har da gaske ya kama mutun shi yake salamawa ya sama ma kansa mafita ba wai Ni a yi tunanin Ni ce zan samawa kaina ba, i love Abdallah, Ni na san da ina son ABDALLAH, kuma zan iya rayuwar aure da shi har karshen rayuwata, ki Kadara wannan abin da kika karanta shirme ne kawai, kin gama bari ki gani....na goge, haka kuma na goge shi daga rayuwata, wace ya aura kuwa ya je ya zauna da abinsa shi ya gano!" Daga nan ta yarda wayar a nan ta fice ta nufi bayin Mah dake cikin dakinta na barci ta bude ta shiga da sauri tana rufe bayin ta saka hannayenta bibiyu ta rike kanta, bugawar da kirjinta ke yi na neman fin karfin ta a hankali ta silale jikin kofar ta sake saka kanta tsakanin cinyoyinta ta fashe da wani irin kuka mai nishin nan, a ranta tana ta astagafari da ambaton sunnan Allah, ayanawa take yi' Allah kai ne Allah, Allah ka cire min abinda ke raina ya zamo kamar bai taba wanzuwa ba a ruhuni na, ya Ubangijin samai da kasai ka saka min soyayar mijina fiye da ta kowa a zuciyata ka bani ikon yi masa biyayya da dukkan lokacina a kansa, ya Allah ka ji kaina idan har ba zan iya manta abinda ke raina ba ka amshi raina na zo gareka tun kafin na kona kaina, ina tawasali da sunnayenka tsarkaka ka tsare Ni da fadawa halaka a kan makauniyar soyaya.....' A falo kuwa, jiki tamkar an zarre mata laka ta zauna kasa tana sauke ajiyar zuciya, a bayane, sai dai muryarta kasa kasa sosai ta ce" RAUDANA, ta wani fannin zan fi farin cikin ace kin watsar din, domin matar da ake maimaita matarsa ce ba zan taba so wani abu ya hadaki da ita ba a rayuwa, dan kuwa kudin iyayenta sun bata dama sosai na daukan duniya a matabata, na ga status din matar ƴaƴanta tana dora yau ne daurin aurenta, buri ya cika yau ta auri sarki? eh lalle abubuwa zasu karu har su wuce da, sam halayarku ba iri daya bace, ita ko gaisawa bata yi da talaka, bata hulda da mace mai muni ko baka, domin ko mai aikinta fara ce kyakkyawa, yarinyar nan ban san a inda ya ganota ba, ama idan ana kiran mutun dan Adam da AZAL tabas itace, tana da raini fiye da tunanin mutun, kuma idan tana waje ta tsani ace wani dan Adam ya fita a wajen, sai ta yi yadda ta yi ya zamo itace sama da uban kowa....., uhum Ni kam ina tausaya masa dan ko Tata mahaifiyar ita ke yi mata biyayya bale uwar miji, da wahala ta girmama mahaifiyarsa....." ( kai, 🤔, Mah,? lalle da an yi kulli kulin kubura da yar mutane muna gefe muna shan lipton) .................................................... "HEY" SHAHEED ya fada a karro na uku kennan, tunda suka juyo suka dawo falonsa suka zauna , yana zaune ne ama tamkar gunki, ga fira a bakin SHAHEED din a yau, ama kuma abokin yin kamar baya cikin duniyar masu rai "Lafiyarka kuwa?" SHAHEED ya fada , fuskarsa na nuna alamun damuwa Rawanin dake kansa ya shiga kuncewa, har ya warware shi ya sauke hular dake ciki hakan ya ba gashinsa damar bayana , ya cire agogon dake hannunsa hadi da kai hannayensa wajen goshinsa ya ringa murzawa, kirjinsa na yi masa wani irin zafi, kwakwaluwarsa na tafasa, hankalinsa gaba daya tamkar ba nasa ba, duniyar kaf ta yi masa kunci fiye da tunanin bawa A hankali ya sake kallon SHAHEED, muryarsa cen ciki ya furta" Ta yarda ta aure shi, SHAHEED ta yarda ta aure shi.........." Daga haka ya dauko wayarsa, kirar samsung wace ake ninkata ya bude sai ga hoton kunshi a hannun mace ya haska saman screen din, a hankali ya shiga wajen msg ya bude ya mikawa SHAHEED sannan ya mike tsaye ya saka hannayensa cikin aljihun wandonsa ya ringa kai kawo yana ta faman kiran sunnan Allah, dan ya sani shi kadai ya isa ya sanyayar masa da zuciya a irin halin da yake cikin nan SHAHEED ya karanta ya kai sau goma, du idan ya karanta kuma sai ya dago ya dubi YUSUF, sai ya sake karantarwar "ya Salam, Dama a gidan nan take? dama a kusa da kai take?" SHAHEED ya tambaya, hakan ya sa YUSUF dakatawa ya dago idannuwansa ya zuba masa, lebensa kuwa ya yi Jajajir ya tasa tsabar yadda yake dantse shi "Na san me zaka ce......, ya yaya ina ji ina gani ko?" YUSUF ya fada yana kallonsa, dan ya sani sarai SHAHEED a kan magana irin wannan kulun fada masa yake yi ya daina kiran soyaya Azal, ya gwada ya gani babu abinda ya kai soyaya dadi a gidan duniya, ama sai ya yi murmushi yace baya cikin wannan gangancin "Koda ta tare sai ya saketa, ina zuwa!" SHAHEED ya fada a zafafe ya mike da nufin fita YUSUF ya yi gaggawar riko alkyabarsa ya dawo da shi yana dubansa a tausashe ya ce" A'a, Please" SHAHEED rai bace yace" Ka san kuwa a wani irin hali kake kokarin saka kanka? ka san irin girman rikicin da kake kokarin nuna zaka iya yi? waye kake son birgewa da nuna wannan halin? mace ce fa, ina mai tabbatar maka koda mutuwa zata yi tana iya rike damuwarta a kanka, ya Salam,, a kan me zaka bari ta aure shi?" "Dan tana son shi!" YUSUF ya fada da muryarsa da take nuna yana daf da gazawa sakin alkyabar SHAHEED ya yi ya juya ya nufi cikin bedroom dinsa ya bude wajen ajiyar magungunnansa ya ciro na ciwon kai ya bude frij ya ciro karamin ruwa ya bale ya hadiyi maganin sannan ya juyo yana kallon SHAHEED da ya harde hannayensa yana kallonsa ya ce" Idan ka ji ana cewa macen da ba za'a iya aure ba, gaba daya itace, dan da ka ganta a nan a kan kudi ko? Sai ta shaki wuyanka, dambe kuwa babu kalar wanda bata yi ba na gani, wanda na yi niya ta ga na ga tana yi nake bari ta gani a lokacin da take yi ama in fada maka ko a kwalar rigarta, kai dai halaya sak na rashin jin magana....ama ban taba jin haushinta ba dan na san dalilin da yasa take cikin wannan halin, SHAHEED tana da yaro , hakan bai taba damuna ba, da ido take min tatas sai dai ka ji ina sauke ajiyar zuciya....., kamaninta yadda ka san flower........" ya karashe yana sauke dan murmushi hadi da tatare girar goshinsa Sai kuma ya gimtse lokaci guda ya ce" Na zata, zata ture, dan kofa saura minti ɗaya a Daura mata shi zan katse, hakan ya sa wayar nan bata fita a hannuna ba sai yanzu da na baka...., ka ga shiru ba msg dinta ba kiranta, da ace bata sonsa koda kadan ne, da ta lalata wannan aure nasu..... shi yasa nace ba zan taba yafe mata ba, ta idasa sakani yarda cewa *SOYAYA ITACE AZAL DINA!*" SHAHEED kasa furta komai ya yi, yana kallonsa ya cire rigar dake jikinsa ya nufi bed dinsa, a takaice ya ce" Please, ka hanna kowa zuwa inda nake, nd wace Hajia ta aura min ta sauka bangaren Mah idan na shirya raba bed dina ta zo!" Daga nan ya rintse idannuwansa, ya ci gaba da juyawa a saman gadon nan abu daya yake son ganni a gabansa a yanzu, itace, ya dubeta ido cikin ido yace nawa take so da har ta iya zabar kudaden cen a kansa? ta san me yake iya bata ko ya mallaka mata a duniya ne? ta san shi me ya mallaka a duniya ne?, yana so ace ya ganta ido cikin ido ta fada masa shi zata sake ba wani jikinta ba shi ba?, zata iya zuwa ta ga wani ba shi ba? ita ai ba yarinya bace, ba kuma makauniya bace, ya tabata a irin yadda ya karanceta ta jima da gane abinda yake ransa, yarda ne bata yi ba bayan shi ya yarda da wanda yake ganni a nata idannuwan? wayo Allah, ya Allah haka azabtar nan take? ashe zafi ne da ita mai karfin gaske? "RAUDA, BA ZAN TABA YAFE MAKI BA!" yake fada muryarsa a shake, jikinsa kuwa ya kama hautsinew da zafin zazabi! SHAHEED , duk murnar da yake na auren abokinsa sai abin ya sare masa, shi da ace zai yarda, walahi a yanzu yanzu sai ta amsa sunnan matarsa, sai dai irin yadda ya kulaceta abin ya bashi tsoro ainun, kuma a yanzu ba zai taba yarda ace da shi laifinsa bane, Bama zai bada damar nan ba in dai YUSUF ne, ba zai yarda cewar shine ya dace ya kwato ta ta yadda ita da kanta ba zata ankara da ta shiga Wajen da fitarta zai yi wuya ba!, sai gashi wani ya riketa a lokacin da bai shirya rabuwa da ita ba Hucin numfashi ya fitar da wayarsa ya yiwa Sarkin bulala texte minti kadan sai gashi ya shigo ya duka kansa a kasa bayan ya kawo gaisuwa wajen aminin uban gidansa sannan ya yi shiru yana jiran sakon mai Damagaran Sai da ya gama daidaita abinda zai isar ya ce" 39 Azl 40 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo Sai da ya gama daidaita abinda zai isar ya ce" tabatar da an hanna kowa shigowa, ka je ka sanar wajen Hajia baba a sauke amarya a bangaren kakar marayu, ka sanar mata umarni ne daga uban marayu!" "An gama ranka ya dade, a huta lafiya, Allah ya karra nisan kwana mai wukar yanka" ya fita yana kirari, shi kuwa ya gyara zamansa ya shiga tunanin yadda zai yi da wannan jirgagen abokin nasa, yadda zai koya masa hakuri da halin mata, ya kuma fada masa sai ana taro su, idan har akace za'a yi da su yadda ake yi da namiji tsaf zasu hada maka cutar da likita zai kasa gani, a zo ana maka dan turare ana fadin ai jifa ne, bayan ba wani jifa a balakin mata ka afka! Sako na isa wajen Hajia da gagawa ta sa aka Hau mota aka nufin gidan su Amarya, a nan cikin gidan kuwa ta sa aka bata wayarta ta yi kiran layin Mah ta sanar mata cewar bangarenta amarya zata sauka maza a shiga shirya mata wajen zama a lokacin da aka sanarwa Mah, sai ta rasa me hakan kuma yake nufi, bangarenta dai bangarenta?, sai ta shiga neman layin YUSUF din, ama bata shiga, dan SHAHEED na tura sakon ya kashe wayoyin dan ya tabata sai an yi ka je ka zo da maganar dan kuwa rigima ce wannan ai yake son saka mutane a ciki! Gannin bata samun layin sai ta saka alkyabarta ta nunawa yar uwarta tana zuwa ta bi ta hanyarsu dake sada su da junna ta nufi bangaren Hajia tana zuwa ta tarda Hajia ita ke taro, domin dankam ana ta Kai kawo tsofafin yan gayu sun cika wajen Hajia gaba da baya sai sha'ani ake na kakar sarki da kawayenta Bayan ta gama gaishe su sai ya je dakin Hajia ta zauna tana jiranta dan ta gabatar ta gane wajenta ta zo mintina ƙalilan tsakani Hajiar ta shigo, ta sha lesh dan ubansu da gold a wuyanta da hannayenta har ga Allah Mah sai da ta yi mamakin yadda aka yi ta iya jure shigar nan a jikinta duba da shekarunta Da matukar girmamawa Mah ta ce" Hajia, dangane da maganar sauke amarya a wajena ne, nace me zai hanna a same shi a ji dalilinsa? duba da yannayin yadda aka saba, lafiya kalau ba a saba kawo amarya a sauketa wani wajen da ba dakinta ba, kar aje wani abinsa ke damunsa ya yanke hukunci haka ya cutarwa yar mutane" Sai da Mah ta dasa aya sannan Hajia ta sauke ajiyar zuciya, itama abin a ranta sai dai ita kam babu abinda zata iya yi a yanzu da ya wuce a bi abinda ya fada din, dan haka da kula ta ce" Kin gane, a sauketa inda yace din, tunda ya yi biyayar nan aka yi auren nan na fi so a bi shi a hankali har zama ya zaunu, idan aka watse sai ku tatauna in ya yarda sai ta je cen din, in kuwa ya kiya sai ta yi zamanta a nan din, kina gani saboda kayan dakin cen sai da na yi kiran mahaifinta da kaina nace masa ya dace ya tsawatarwa duk wani mai son sako min kace nace a tafiyar nan, domin ba zai taba yiwuwa ba a saka shi surutu a kan abinda ya yanke, da yace kar a zo masa da komai dan gardama da nuna ana da shi sai da aka zo din , Ni kuwa na saka an sauke a cen dan ba zan taba bari ya sani ba Ni kam!" sosai ta yi mamakin wasu kalamai a furucin Hajia, sai dai bata nuna ba ta mike ta koma bangarenta ba tare da ta Musa ba, ama abu daya ta sani idan har ta same shi kafin a kawo matarsa babu mai sauke mata ita a bangarenta gaskiya, ta yaya zata iya zama tare da sarakuwa?, a'a kar ya fara yi mata haka, bata din fitina ita kam su je cen su shirya kansu su tatali junnansu A gidan su amarya biki bidiri, a nan ake bikin mai sunnan biki domin babu ce kawai babu a wannan rana, dan tun daga kan uwar amarya har zuwa autar gidansu babu wace bata cenza tufa sau biyar zuwa wannan lokacin ba dama bikin gidansu haka ne idan aka ce ana sabgar da ta shafe su zaka ga sunna cenza tufa tamkar a cikin rijiya suke janyo kudaden siyansu makida kuwa kala kala tun daga na Nijar har na makotanmu wato Nigeria sunne ke wake ahalin gidan baki daya da wakokinsu kala kala na amaryar da angonta Ana cikin wannan shagalin sako ya iso masu cewar idan an je da amarya a bangaren mahaifiyarsa za'a ajiyeta yayar Amnah ce aka fara sanarwa sakon, a gigice ta mike daga wajen kidan nan ta nufi ciki tana fatan samun mahaifiyarsu dan bata jima da komawa ba daga wajen kidan ta fito ta zuba cefa iya cefa a lokacin da ta sameta tana cikin kawayenta bata sanar mata ba sai da ta kirayeta ciki, dan a rayuwar da suka saba da mahaifiyarsu ta koya masu ko aminanta bata lamunce su ji sirinta ba bale mutanen gidan da zagaye sunna shiga ta sanar mata wannan bayanin da ya saka uwar yin turus kafin ta dan yi wani yannayi da fuskarta sai kuma ta kai wajen kujerar dakinta ta zauna tana fadin" Bani wayata na yi kiran Hajia, a'a fa, ba zai yiwu ba, dama ta fada min in shirya Amnah sosai dan uwarsa ta fi karfinsa ta gama shanye shi sai yadda ta yi da shi, dan balaki Bama zata bari ta je dakinta daren farko ba sai dai a sauketa a wajenta? ta yi mata uban me? a'a fa, kar matar nan ta saki ta shigo lamarina dan na yi watsi da ita baya ce min komai a kan yarinyata, kuma tunda Amnah ta nuna ta ji ta gani tana son sa an gama, sai dai ya manta da ita uwar tasa ba dai Amnah ba!" wayar ta miko mata, cike da isa ta danawa Hajia Rufaidah kira , wato mahaifiyar su Salima, ita ta sani a famillyn, tare suka yi karatu, kuma a rayuwa ta yau da gobe idan wani abu ya same su sukan ziyarci junna, a yanzu da maganar auren nan ta kullu kuwa sai zumunci yake son dawowa sabo dal , saboda Hajiar ta fada masu gaskiyar lamari cewar sai sun yi da gaske saboda mahaifiyar Malik muguwa ce , kiri kiri su ta raba su da mijinsu, haka kuma d'anta ta gama shanye shi sai yadda ta yi da shi da takama, kalar yadda take ji da kanta a matsayinta Na matar gagarumin mai kudi ta amsa salamar Hajia, ta dan ja iska cike da isa ta ce" Hajia, yanzu magana ta zo min, kishiyarki tace wai a part dinta za'a sauke Amnah, ta san kuwa da wa take tafe?" Hajia da bata san bama maganar sai da ta mike zaune tana mutsike idannuwanta saboda tun dazu ta shige da nufin zata yi sallah ta yi kwonciyarta tana hutawa dan ta gaji sosai da hayaniyar nan gashi yanzu komai ya zama na balaki jiranka kawai ake yi a ga ka yi wani abin yanzu a rikita maka lissafi A nutse itama da kalar nata isar ta ce" Wai Ameerah din ta fadi haka?, yaushe kuma?" cike da basarwa irin ta masu kuɗi ta ce" Yanzu mama ta zo min da maganar, Hajia ba da zan yarda da abubuwan nan ba fa, gaskiya na san darajar yayana kuma mun san yancin kan mu, tun kafin ta shiga zata fara gasa mata aya a hannu?" Hajia ta tabe baki tana gyara zamanta ta ce" Kadan kika gani a tarin muguntar matar, idan kika yi wasa sai an rikita maki lissafin yarinya kuma tana ji tana gani sai mijin ya gagareta!" "lalle, uhum....lalle, sai dai ita d'anta ya gagareta, zan yi kiran ki Hajia, ama ki shirya tarbata dan kuwa tunda na ji haka nice zan kai AMNAH dakinta!" ta datse kiran tana wani murmushi abin tsoro tana kada kafa ta dubi mama, wato y'arta mai sunnan mahaifiyarta ta ce" Mama, je ki ce a yi a tashi kidan nan AMNAH ta shigo da wuri dan a shiryata da wuri, in sha Allah Ni zan kaita dakinta" Wucewa Mama ta yi tana ta kada mazaunai tana tunanin ai Bama zai yiwu ba walahi ace za'a tafka masu wannan rashin mutuncin, ina , sun shirya tsaf shiga gidan nan ba dan su fito kwana kusa ba! kuma duk wata matsala dake iya Kunno masu a shirye suke tsaf da tararta ko Wacece! Yama na yi aka shiga hada hadar kai RAUDAH bangaren Hajia Mah da yan uwanta ne suka kai RAUDAH suka mikata hannun Hajia sannan suka koma falo, domin wankan amarya Hajia ce zata yi da kanta da shirya amarya, shirin da sun sani ba'a digawa amarya ko kwali bale a yi zancen wani mak'up na rashin tsari, domin Hajia a kulun takan kalubalanci irin rayuwar nan, takan ce ina anfanin wannan rayuwa ka wanke budurwa zaka mikata dakinta ka bari a kwaliye mata fuska kamar wata wace ta gama watsar da kanta a titi? Su dai sunna waje suka yi salolinsu na magariba sannan aka shiga har fira ana jiran isha A cikin dakin Hajia kuwa Rauda na cikin wani hali na matsanancin mutuwar zuciya da tunani, sai dai tunda Hajia ta zo hankalinta ta koma kan Hajia, domin, tunda take magana ta kusa da kusa bata taɓa hadaya da Hajia ba, Hajiar dai ta santa itama karya take tace bata san Wacece Hajia da dukkan sauran halayarta ba, sai dai a yau sai take ganninta daban, bale da aka gama yi mata wanka irin na amare Hajiar ta bata wata jalabiya da hijabinta ta umarce ta ta saka ta yi sallah, bayan ta gama ta umarce ta kan ta hau abin kanshi, ta hau ta yi zaune a nan ne Hajiar ta shiga yi mata nasiha, kwarai nasiha ce, nasiha ta zaman duniya wace idan ka yi abinda aka fada maka lalle ka tanadi harda ta lahira, domin bata taba tunanin Hajia zata dubeta ba bale wai har ta damu da yi mata nasiha da fada da kakkausar murya a kan aure da darajarsa sai da Hajiar ta dubeta ta sanar mata a yanzu darajarta ta karu, idan har ta kiyaye ta yiwa mijinta biyayya lalle ita ke da riba, ribar dake iya shafar su su marikanta, Hajia ta yi mata nasihar da uwa da uba ke iya yiwa ƴaƴansu, a lokacin da ta zo rufe magana tana dubanta ta ce" RAUDA, ke jikata ce, ke din ahalina ce, ki rike mutuncin kanki, aure shi ne darajar da Allah ya luluba maki, ki kuma da shi sosai ki tsira gobe kiyama" Hawayen dake zubo mata suka sake wanke mata fuska, Hajia ta yi murmushi tana kallonta, bata taba jin mutun ya shiga ranta irin na yarinyar nan ba, yau kafin ta yarda ta cire rigarta ta zauna da sket karami da breziya a yi wankan nan na nonon raƙumi sai da Hajia ta yi mata jan ido, kuma ana yi tana kuka, ba kamar wasu daga cikin ya'yan gidan ba, ana zuwa suke tubewa tik sai Hajiyar ta ce su rufe ba fa tik zasu yiwa mutane ba, kuma idan ana wankan nan ana yi sunna fadin inda bai samu ruwan ba, kuma har a yi nasiha a gama kiri kiri sunna kallon mutane , ama y'ar nan tunda aka fara har kawo yanzu da Hajia ta yiwa Mah magana ta shigo kuka take yi kanta a sade du ta fice a hayacinta Hajia ta yi murmushi tana kallon Mah, a tausashe ta ce" Yaya aka yi baki zo min maganar filinta da nake ba jikokina ba idan zan aurar da su?" da mamaki Mah ta kalli Hajia, sai kuma ta yi murmushi ta ce" A yi hakuri Hajia mantawa na yi" Hajia ta yi murmushin itama tana kallonta ta ce" Na yi, ama gobe gobe ki zo a fitar da takardar ta a ba Uban marayu ya saka hannu a bata, sannan ki kaita dakinta da kanki dan Allah, Allah ya baki ladan riko" Mah ta karra kamuwa da mamaki mai girman gaske, tana amsawa ta kama RAUDA ta mikar da ita, Abin mamaki Hajia ba biye da su har wajen mota tana sake fadin a kula da ita, sannan ta tabatarwa Mah zata karbi amaryar Malik idan bata dawo ba har aka kawo ta , dukda a yadda al'ada take babu wanda ya isa ya san da shigowar amaryar, ama kuma sun ce wai zasu yi ko amaryar doka ko me?, zata je dai bangaren na Mah ta tarbi amaryar kawai Tun a wannan lokacin motocin tafiya da RAUDA suka fice a gidan, ciki harda aminiyarta da Salima, da sauran jama'ar dake nan dan taya Mah murnar aurar da y'a, Bah kam da Aba an ce zasu ganta idan aka kawo ta sati da ake kawo amarya ta wuni gidansu a yi mata kunshi da kitso, Hajia tace idan an kawo ta zasu yi mata nasihar su ta iyaye maza Tunda motocin Su RAUDA suka fita , Hajia ta juya da nufin komawa bangaren Mah aka shiga shelar a marmatsa za'a shigo, sai ta dan ja ta juyo dan hangen mai shigowar ko Malik ne domin yau a idonta bata ganshi ba, rabonta da shi tunda asubahin nan kade kaden da suka fara shiga kunnayenta suka sakata sake maida hankalinta tana mamakin waye kuma da kida? Bayan tun na daurin aure da aka yi aka soke kidan akace kar a kuma shima na daurin auren ba zata suka yiwa mutane, rasuwar marigayi ba wani jimawa ta yi ba, ya kamata ace an tsagaita wasu abubuwan, shi yasa wunin an yi shi na biki ne kawai ama ba wasu kade kade da abubuwan nan na sabga jerin motocin dake shigowa da irin iface ifacen da suka shigo ya tabatarwa hajia ko su waye Wadinnan baki ne a masarautar nan da har zasu zo su yi wannan rashin da'ar a irin wannan lokacin bata gama mamaki ba aka ringa fitowa daga mota, yannayin ado da kwaliyar matan dake fitowa ya fadar mata da gaba da sauri ta juya wajen da ta ji murya kamar ta dan daudu yana fadin" Ku gafara a bude motar Hajia, hajiarmu maganin kukanmu, tabas mun yi kamu, kuturun kare, wannan gidan ko a Saudiya ai ginane ne, jama'a ga inda ake barin kudi da sarauta, Ni na san AMNAH dinmu sai ta yi baban kamu, sarki kika dauka tawa fito mu kashe, sarkinma uban sarakai ne dan uban mutun!" Kiris ya hanna Hajia summa, a lokacin da ta ga an bude bayan wuleliyar motar nan wata ta fito da doguwar riga ɗinkin nan da ake yiwa amare na yanzu, daurin kalabin kanta yadda ka san panka haka ya bude, hannunta rike da wani abin fifita, kafarta sanye cikin dan uban takalmi takani na karye!, a lokacin da masu daukan vidion da suka zo da su da masu hotuna suka shiga gabatar da aikinsu, a lokacin ne wannan zabiyar yan daudu ya kuma bude baki yana fadin" MRS YUSUF BELLO kennan, AMNAH, yar kudi, jikar kudi, yanzu kuma ta gama gogewa Yan uba harda ta zama matar kudi, kuma matar SARKI, yau dole mu tsole idon makiya da yan yatsunmu, ku kauce uwarku ce ta karaso!" har ga Allah, ashariyar da ya kyatsa sai da Hajia ta rintse ido, gaba daya sai ta ji kamar ita daya ya ware ya durawa ashariyar nan...... , LA'ILA HA ILALAH Muhammadu RASULULAH Sallallahu alaihi Wa sallam 😭😭😭😭😭 wayo abu ya same mu, ku zo mu jajanta Hajia me kika dauko mana? ... a ringa yi ana amsar bonanza😭😭😭 Azl 42 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo A hankali Rauda ya furta" ABDALLAH? Kai ne?" jin shiru ba amsa, ya Sakata yin adu'a ta sake kunna sauran fitilun dakin ta nufi gadon tana tarare hijabinta ta hau hannunta na rawa ta yaye bargon tana Kiran sunnan sa, domin tana yayewar fuskarsa ta bayyana da shadar dake jikinsa , sai uban zafin da jikinsa ya dauka tamkar garwashin wuta hankali tashe ta ajiye wayar tana sake kiran sunnansa ta ce" Abdallah, dama kana cikin gidan? Baka da lafiya ama ka kasa fada min?" Da kyar ya bude idannuwansa da suka yi kore sharrr ya sauke dubansa a saman fuskar ta murmushi ya kakaro da kyar yana fitar da huci a saman lebensa ya furta" An kawo min ke? Alhamdulilah ya rab da ka amince min har na ganta a dakina, wifey zo , zo jikina Please" Kasa zuwan ta yi, saboda bata taba aikata haka cikin hayacinta ba, sai dai kallonsa take yi tana murza yan yatsunta muryarta a raunane dan yannayin idannuwansa sun rikitata a hankali ta ce " Ka tashi mu je asibiti Please, ka tashi" Nokewa ya yi yana kallonta ya ce" Na ki din, dan kawai yan lokutan da suka rage min su kare min ina barci, dan na tabata idan na je allurar barci zasu maka min shikenan na yi asara na tafi ba tare da na kalli fuskarki ba?, Please zo jikina, kin ganni fa, babu abinda zan iya yi maki koda a tsaye nake, zo in rungume ki, kin manta kin ce min idan muka yi aure zaki rungumeni da kanki, dan Allah ki ture kunyar nan da kike ji kin ji?" RAUDA ta ji hankalinta na neman tashi sosai, a tsorace take kallon sa, irin yadda ya dage sai ta shiga jikinsa kuwa wata irin kunya ce ta gaba dabaibaye ta, kana ganninsa kuwa zaka tabatar da yana cikin matsanancin hali ne, dan haka ta rasa yaya zata yi masa, gaba daya ta mike ta ringa bincikar wayarsa a dole sai ta ga numbar likitansa , lokaci daya tana tambayarsa numbar likitan nasa? maimakun ya fada mata sai yace da ita dan Allah ta taimake shi ta yi masa kiran numbar Mah shatakai ta tsaya tana kallonsa, sai dai gannin ya ja wani irin numfashi kanta ya sara ta shiga saka numbar Mah , a lokacin kuwa Mah din sunna hanya dan sun ajiye Atu kennan za'a nufi gida da su wayarta dake hannun Salima ta yi ta ringing Salima ta duba mai kiran, tana ta sake dubawa kamar numbar Abdallah dan haka sai ta daga tana mikowa Mah ta ce" Mah kamar numbar Abdallah" Mah ta amsa tana fadin" ABDALLAH kuma?, hello asalamu alaikum" RAUDA ta yi iya yinta dan ta yi magana sak ba tare da ta yi kuka ko gargadar murya ba, ama abin ya faskara A hankali ta furta" Amen wa alaiki salam Mah, Rauda ce" Mah ta yi saurin fadin" Babu, kuka kike yi? lafiya?" RAUDA ta sake juyawa tana kallonsa, a hankali ta ce" Mah, Abdallah ne, bashi da lafiya kuma yace a yi kiranki wai" Mah ta ji gabanta ya fadi, tana kallon direban YUSUF ta ce" Mu koma gidan baby, baby ganinan ki zauna ki daina kukan ganinan in sha Allah" RAUDA ta ja numfashi sai kawai ta fashe da kuka ta juya tana kallonsa lokaci daya tana sakin wayar nan ta koma saman gadon a hankali ta karasa inda yake kwancen a hankali ta bude hannayensa ta shige jikinsa, jikinta na rawa ta rintse idannuwanta, muryarta na rawa ta ce" Ka manta, ka ce min RAUDA in dai ina raye, ba zaki yi kuka ba, Nine mijinki, Nine yayanki, Nine komai naki, to menene kuma kaima kake wani abu kamar wanda zaka bar Ni? shikenan Ni duk wani makusanci nawa sai na rasa? Abdallah, kar ka yi min haka Please" Murmushi ya yi, a hankali ya sake rungumeta a jikinsa, ama bakinsa ya gaza furta koda a ne, dan sosai abin ya fara motsawa, sai dai yadda yake jinta a jikinsa ya zame masa wani nau'in salama a cen cikin zuciyarsa, wato zuciya da abinda take so A bangaren Mah kuwa direba na tuki kamar zai tashi sama, ita kuwa tana tambayar Salima da tace ko ciwonsa ne ya tashi cewar wani ciwo fa? wani irin ciwo? Salima ta yi tsuru tsuru, dan RAUDA ta yi mata magiyar kar ta sanarwa Mah a lokacin da Salimar ta san cewa yana fama da matsanancin ciwon zuciyar da likita yace idan har bai yi gaggawar zuwa aka cenza masa ba tabas kowani lokaci yana iya mutuwa, shi kuwa yace ba zai yiwu ya je a Barka shi a cire masa zuciyarsa ba a saka masa wata bayan a cikin kashi dari daya ke rayuwa da irin aikin nan, salon ya yi biyu babu, a lokacin nema ta ji matsalarsa ta rashin haihuwa kuma a ranar ne ta gane Rauda wannan ba damuwarta bace dan itama burinta kennan rashin haihuwar "Salima?" Mah ta fada a lokacin da motarsu ta shiga katon get din gidan tana kallonta Salima ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Mah, yanada ciwon zuciya ne, wanda ya kai matakin karshe, shine nace ko shine ya tashi?" Dif Mah ta yi tana kallon Salima, ciwon zuciya? matakin karshe? subahanallah, kuma yake zaune bai je asibiti an masa aiki ba? kasa cewa komai ta yi ta bude motar ta fita har tana buge kafarta saboda tunanin halin da Rauda ke ciki ita kadai da shi, domin ko masu aikinta ba'a kawo ba Bah yace wai sai ta yi sati a gidanta an kawo masu aiki Salama Mah ke yi tana kiran sunnan RAUDA, hakan ya sa RAUDA mikewa a hankali ta sake juyawa ta kalle shi, sai ta ga ya sakar mata murmushi kasa kasa ya furta" zaki iya kama hannuna na dan daga?" RAUDA ta gyada kanta, a nutse ta dauki pilow biyu ta jinginar masa a jikin bed din sannan ta kama shi da kyau ta jinginar da shi a jikin pilow din ta gyara masa bargon sosai a kaffafuwansa, shi kuwa yana Binta da murmushi a hankali ya furta" Wannan kashin turaren naki akoy dadi, kin ji shi a hannayena har yanzu" Ita dai bata tunanin kanta na iya daukar raha ko gane rahar da yake yi mata , har sai da ya sake fadin" Ki sanyo su nan Please" Sannan ta sauke ajiyar zuciya ta fice Tana fitowa ta ga Mah tsaye, Salima a gefenta, ga dukkan alamu ita suke jira, ajiyar zuciya ta sauke a sanyaye ta karasa jikin Mah da ta mata alamun ta zo A tausashe sosai Mah ta ce" Jikin nasa ya tsananta ne kike kukan nan?" Da kyar RAUDA ta iya budar bakinta, tana haki tamkar zata summe ta ce" Mah, Ni dai na ga yana ta wani iri, wai yace a kirayeki" Mah ta furta" Ok,ki ce masa na zo" RAUDA ta sada kanta ta ce" Baya iya tashi fa, da kyar yake magana, Mah baya iya tashi shi yasa yace ki je" Bah ta lumshe idannuwanta saboda gabanta da ya fadi Da kyar ta boye damuwarta ta mika hannunta ta amshi wayar dake hannun Salima ta ce" Bari na sanarwa babanku dan ya sanarwa Hajia kar ta ga mun jima" Kai Rauda ta gyada, sannan ta karasa wajen Salima suka zauna Salimar na rike da hannunta tana fada mata ta daina kukan nan in sha Allah ba komai bane zai mike haka masu ciwon zuciya suke Gannin ta kasa samun numbar Bah ana ce mata a kashe sai ta yi kiran ta Hajia, wace jimamin abinda take ciki ya sakata kasa gane jimawar da su Mah din suka yi, tana cen tana ta neman mafita a falonta ta daga kiran a tausashe ta furta" Andiya, kin dawo ne?" Mah ta sauke ajiyar zuciya, a tausashe ta sanarwa Hajia basu dawo ba, har sun kama hanya kuma ga abinda yake faruwa sosai hankalin Hajia ya tashi, ga tarin mamakin Mah sai ta ji tana fadin" Bari in nemo Bellon, idan ban ganshi ba kuwa zan sa a min iso wajen Malik dan na zo , kafin nan ku yi kokarin sada shi da likita, Allah ya bashi lafiya" Mah ta amsa jiki ba karfi ta datse kiran, sannan ta dubi su Salima ta masu alamun su yi gaba gaba na baya suka shigo dakin, a lokacin ya saka abinda yake tarawa idan yana tari ya gama yin tarin kennan yana goge abin jinnin da ya bata masa baki ya yi gaggawar cirewa daga bakinsa da sauri ya so boyewa, sai dai karfin jikinsa bai bashi dama ba ya saki abin a kasa, gashi du yadda ya so dagowa dan ya dauke ya kasa, hakan ya sa RAUDA da ta zubawa abin ido karasowa ta duka ta dauka ta bude kusan a tare suka juyo suka zuba masa ido, Mah hankali tashe ta karaso tana fadin " Subahanallah, jinni ne daga bakinka?" RAUDA kuwa sai ya kai zaune a nan kasa ta zuba masa ido, gannin yadda ya sada kansa , kunya ce ko menene? ya dai ƙasa kallon Mah ido cikin ido har sai da abin ya lafa masa ya dago yana duban Salima a hankali ya ce" Sister, Please daukowa Mah kujera Gatacen, nd ki bani wancen akwatin dake saman dayar kujerar" Salima ta juya ta cika abinda ya ce din jiki ba karfi Akwatin da aka ba Mah ta bude ta ringa fitar da takardu na dukiya daya cikin daya cikin daya, da wata takarda mai dauke da code na banki, da ky cike a akwatin, sunne suka saka akwatin yin nauyi sunnan dake saman kowace takarda ya sakata dagowa, itama zuwa lokacin nata hankalin ya fara matukar tashi yana kallonsa ta ce" me kennan?" Abdallah ya sauke ajiyar zuciya a tausashe , murya a jinyace ya ce" Zan so ace, tun ina cikin hayacina na cika abinda nake son cikawa, domin ke da kanki kin san idan aka zo wannan gabar kuma sauran saura ne, dan Allah ku yi hakuri, ba aurar maku yarinya bayan na san abinda nake ciki, da ace bata yarda ba duk irin yadda nake da burin aurenta ba zan tirsasata ba, Ni dai na san ina sonta domin Allah, shi yasa tunda na san da wahala ta rigayeni barin duniya na yiwa kaina wannan alkawarin na dukiyata itace maganarsa, Ni bani da dangi, koda ina da su ban san inda suke ba, basu san ko akoy Ni a duniya ba, iyayena sun yi aure ne irin na yawon duniya, mahaifina ya auri mahaifiyata, kuma Allah ya yi basu jima da auren ba suka koma ga mahaliccin su, dukiyata ta halal ce, ba gadonta na yi ba, nema na yi da zufata har na kai inda na kai, tafiyar nan da na yi na tataro komai nawa da burin yin rayuwa mai dan tsayi da ita na dawo nan kuma na yi shige da ficeta da lauyana an min abinda nake so, sai dai kashhhh, tunda satin aurenmu ya kama na zama ganinan, a kulun baya lafiyata ke yi, ko yau daurin auren nan da kyar makotana suka kamani muka je,ana gama daurawa na samu na dawo dan ba zan so ace tana cikin taron nan an je mata da maganar na fadi" "Ya Salam, Abdallah, ama ciwo ai ba mutuwa bace ko? dan Allah ka daina magangannun nan mu je asibiti, ke ku tashi ku fadawa direba ya zo ya kama mana shi mu je asibiti" Mah ta fada tana tare hijabinta tana tare kukan dake son kwace mata, dan yadda yake magana yana jan numfashi ta bakinsa ko baka da imani sai ka tausaya masa bai hanna su fita ba, sai dai sunna fita ya dubi Mah a lokacin da mike jikinta na rawa ta sake shiga neman layin Hajia ya ce" Mah, ciwona ya zama Cancer fa, dan Allah ku bar Ni na mutu a saman gado........................" A lokacin ne kuma Mah ta juyo da sauri tana kallonsa, ta ki cewa komai sai nunawa direba da ta yi ya dauko shi su je, dan walahi ba zata taba iya barinsa a haka ba Hajia kuwa sunna gama waya da Mah ta saka baban hijabinta itama tana neman layin Bah ama bata shiga hakan ya sa kawai ta nufi Part din Malik da fatan Allah ya sa bai kwonta ba, tare da yan rakiyarta sunna karasowa basu tsaya kiraye kiraye ba suka bude mata ta wuce ciki a bakin kofar nan mai madubi ta tsaya ta buga sannan ta murda ta shiga A kwonce da yake idannuwansa kawai ya dago ya sauke a kanta sannan ya lumshe yana godiya ga Allah da ta zo a daidai lokacin da yake da bukatarta Karasawa Hajia ta yi, ta zauna a kujerar dake daf da shi a sanyaye ta furta" Yau ko a leka Ni? Malik wuni guda?" Shiru ya mata dan ya san dama sai an masa yan jaje, Idannuwansa ya dago jin ta ce" Yaya muka ji da wannan sabuwar masifar? yau Ni Hajia Azal ta fado mana gida, Malik ba zan so ka ga yarinyar nan ba, kade kaden nan fa da ka ringa juyowa su ne, Ni kam safiya na yi ka saketa ta je gidansu, ba matar jikana bace y'ar nan ido a tsakiyar kai!" Murmushi ya yi ya sake dago da kansa yana kallonta, kasa kasa sosai ya furta" Ta fado maki dai, kuma ba inda zata je!" "na'am? me kace?"Hajia ta fada tana dubansa, dan yadda ya yi murmushin kamar wanda zai datsa mata magana domin haka yake yi mata lokuta da dama kai ya cire ya ki bata amsa, a nutse ya ce" Bani da lafiya fa, kuma ina jin kamar wanda zan mutu, kin ga jikina karra rikicewa yake yi fa!" a tsorace ta kalle shi, da sauri ta mike gabanta na faduwa tana sake duban yadda ya ringesa, ta kai hannunta wajen wuyansa, ai kam da gumi jikin nasa sosai dan haka ta nemi rikicewa tana fadin" Na shiga uku, ka ga cen wai mijin RAUDA ne akace ba lafiya shine na zo sanar maka ka sa a kai Ni, kuma sai in ji wai kana min zaka mutu?" Idannuwansa dake lumshe ya bude a kanta, sosai ya so yin magana, sai dai ya rasa me zai ce, ya so maida idannuwan nasa ya rufe wayar Hajiar ta sake daukan kuka a tare suka kalli wayar, Hajiar ta duba da kyau tana kankance idannuwanta ta ce "AMEERA din ce, bari na ji?" Hajia ta daga kiran ta saka a amsa kuwa, sai ta ji Muryar Salima tana dirzar kuka tana fadin...... 😭😭😭😭😭😭😭😭 Salima na dirzar kuka take fadin" Hajia, walahi fa inaga ya rasu innalilahi mun shiga uku!" Hajia na tsaye ne, sai gata a zaune ta zube, idannuwanta na wani iri muryarta na rawa ta ce" Ke kuwa wani irin kina ga, dan Allah bani ANDIYAR!" YUSUF dake ringeshe ya yi niyar dagawa Hajia hankali ne sai ya mike zaune yana kallonta , jin ta ambaci Andiya, kuma maganar rasuwa Hajia walahi ita Raudarma ta summa, kuma Mah gatanan tana kuka, shine na yi kiranki dan walahi walahi Mah ta rufe shi ama direba ya taho gidan yanzu " Me Hajia zata yi banda kwasar kuka, hannayenta saman kai wiwi take fadin" Mun shiga uku mun lalace wayo jikata ta rasa miji, innalilahi yau na yi wani rashin, la'ila ha ilalahu Muhammadu RASULULAH Sallallahu alaihi Wa sallam " "Wai meye haka wai?" ya fada da dan karfi dan yadda Hajia ke rizgar ihu a kan abinda ba'a wani tabatar ba kuma bayan ba kyau yiwa mamaci irin kukan nan ya saka shi katseta yana mikewa tsaye hankali tashe Hajia tace" YUSUF wannan yaro balaraben nan da ya gaisheni, shine ya rasu,dan Allah ka sa a kai Ni ka ji?" Gaba daya jikinsa sai da ya mutu, a hankali ya koma ya zauna yana daukan wayarsa ya yi kiran direbansa amintace jim kaɗan ya daga da salama a ladafce ya ce" Allah ya taimakeka gani na shigo dan na iso da sako, Allah ya yiwa mijin Hajia karama rasuwa, na baro su Mah a cen dan na zo na ji abinda zaka fada" Ya jima wayar a hannunsa, zuciyarsa na tsintsinkewa kafin a hankali ya furta" Allah ya masa rahama, ka wuce ciki a je da likitoci su duba shi da kyau, idan sun tabbatar a gyara shi a zo nan da shi , idan bai rasu ba maza a kawo shi in yanzu za'a fita da shi a min magana" Daga nan ya kashe kiran yana kallon Hajia take ta margaya kai taba sharar hawaye ajiyar zuciya ya sauke, sosai jikinsa ya mugun mutu, dukda a bincikensa ya san da ciwonsa da irin matakin da ya kai domin Taj sai da ya je har wajen likitansa, da likitan ya ki fadin sirrin abinda ke yawan kai Abdallah wajen nasa sai da aka sada shi da YUSUF din sannan ya fada tun a nan ya ba masu gadi damar duk lokacin da ya zo su bar shi ya shigo, sannan ya dauke kansa a kan duk wani shige da ficen su sai na ranar da ta shigo da dare nan ya ji haushin abin, shima a lokacin dan Hajia ta gama guma masa tashin hankali ne na wai ita zata zabar masa matar aure A nutse ya ce" Ki yi hakuri, idan ya rasu baya bukatar koke koken nan, ki masa gatan da kike yiwa iyalinki a kwana ana nema masa gafara kin ji?" Hajia ta sauke ajiyar zuciya a zaunen da take hannaye bibiyu a fuskarta, a raunane ta ce" Allah ya masa rahama, yarinyar nan ke bani tausayi, ina matukar tausaya mata, tana son mijinta, gashi yarinyar akoy tarbiyya da mutunci, ashe ba zasu rayu da mijin ba? rasuwar miji baban tashin hankali ne a rayuwa, Allah ya bata dangana da hakurin rashinsa " Idannuwansa ya lumshe har Hajia ta gama ta mike tana sake tambayarsa jikinsa Da hannunsa kawai ya mata alamun da sauki, ta so sakawa a kirawo likita ya nuna ya bar shi, hakan ya sa ta fice ta tafi ta shiga neman layin baban malamin fadar dan ta sanar masa, sosai take tsaye kan lamarin sai bugawa take tana fadin mijin jikarta ya rasu, nan da nan har an shiga kai kawon taya zama a cikin daren nan, abu da masu hannu da shuni TABAS RAUDA ta yi rashi a karro na biyu, rashin dake girgiza duniyar wace ta rasa, rashin da koda babu soyaya sai an girgiza, ita din ta girgiza, domin a lokacin da aka iso da ita a motar asibitin fadar bata san inda kanta yake ba, a lokacin kuwa su Bah sun ji, uncle dinta kasa rike hawayensa ya yi, hankalinsa ya yi mummunan tashi, ya rasa inda zai tsoma ransa danma yana tare da mutane ana ta dannarsa, ama haka ya kwana ya je cen inda RAUDA take, ya dawo inda aka shinfide ABDALLAH RAI KENNAN, BAKON DUNIYA, MUNA SON KA SAI KA FITA A LOKACIN DA AKA DAUKAR MAKA, ALLAH LA BAMU KYAKKYAWAN KARSHE Tun cikin dare ta farka, sai suka yi mata allurar barci saboda kukan da take yi, Mah kuwa tana wajenta tare da Salima, Atu kuwa tunda duku duku ta karaso itama tun cikin daren mijinta ya fada mata, kwana ta yi tana kuka idannuwanta sun yi luhu luhu, duk idan ka kalle su sai ka tausaya masu Da sassafe ta kuma farkawa, wannan karron ba da kukan ba, ama kuma idannuwanta ko bude su bata iya yi muryarta cen ciki ta furta" Mah, har an yi sutura?" Mah ta girgiza kai A raunane ta ce" Mah a kai Ni na masa addu'a kin ji?" Atu ta sake sada kanta wani kukan na kwace mata, hakan ya sa ta fice a dakin, Mah kuwa ta yi jarumta sosai ita da Salima suka maida mata zumbulelen hijab dinta Mah ta sa aka kawo mota har cikin asibitin suka shiga su hudu aka nufi bangaren Hajia da su, inda gawar take Sunna zuwa Mah ce kadai ta rike hannunta suka shiga wajen da gawar take A lokacin ana idasa shirya shi, fuskar nan tasa luwai luwai sai sheki take yi , idannuwansa a lumshe suke kamar wanda yake barci Tunda suka shigo YUSUF ya dago dubansa ya sauke a saman kansu ya ji wani irin tausayinta wanda bai taba ji ba a nutse ya dauke yana jiran ya ji ta barke da kukan da ta saba, sai ya ji shiru har ta karasa gaban gadon da yake kwonce a hankali ta ɗora lebenta saman goshinsa ta mana masa kiss, fari farin furfurar gemunsa ta dan zubawa ido kafin a hankali ta furta" Allah ya maka rahama mijina" Mah ta lumshe ido, hawaye suka biyo kumatunta, ta sake kama hannayen RAUDA ta juyota tana kallonta a hankali ta janyota jikinta ta rungumeta, sai ta ringa sauke wata irin ajiyar zuciya hawaye na bin kumatunta a cen ciki ta furta" Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une" Daga nan suka koma bangaren Mah, wanda ya fara daukan mutane domin tunda asubahi gidajen rediyo aka fara sanarwar rasuwar, da kuma wa'inda aka kiraya aka sanarwa, AMNAH kam dala a bangaren su Salima ta kwana, kuma bata cika tashi da sassafe ba, shi yasa bata san abinda ake yi ba har aka fice da gawar Abdallah aka kai shi makwoncinsa na gaskiya Sai kusan karfe biyu na rana ta farka a barci ta sauko daga saman gadon maman su Salima ta nufi bayi ta yi wanka ta dauro tawul din Salima dake bayin rataye wanda ya jima nan rataye domin ko ita idan ta yi wanka a yanzu ba zata yi anfani da tawul din nan ba sai ta wanke shi, ama ita ta ratayo abinta ta fito tana jin yinwa na neman yi mata ila suka hade da Salima wace ta zo daukan wayar maman nata da ta sakata zuwa ta daukar mata domin sunna cen bangaren Mah gaba dayansu harda Hajia baba , dan tunda Hajia Baba ta je suma suka je babu wanda ya tashi tunda basu ga ta tashi ba kallon kallo suka yiwa junna, Salima da bata santa ba ta ce " Bakuwa muka yi banda labari, sannu da zuwa" AMNAH ta sake duban Salima sama saman nan ta ce" Yauwa, Please a kawo min abinci i'm hangry, ina Hajia ne ta shiga ko tana falo?" irin yadda take magana tana wani kalkaltu ya saka Salima yin sororo tana kallonta, sai kuma ta ce" Ta tafi bangaren Mah wajen makokin mana baki sani ba? " Tana bata amsa ne dan ta ganta tsamo tsamo a dakin mahaifiyarta, ta tabata ko Wacece ta kusa ce dan haka kawai da wahala ka iya ratsa falo biyun nan ka iso nan kuma har da anfani da bayin dakin, lalle ta kusa da kusa ce "Rasuwa? a ina aka yi rasuwar kuma? Yaushe?" Ta fada tana dakatawa daga niyar cire tawul din da ta yi zuciyarta na rawa dan bata son ta ji maganar mutuwa, ko kadan bata so, abinda ta ki jinni a rayuwarta kennan, idan ta ji maganar mutuwa sai ta tsani wanda ya mata maganar ta daina yi masa magana sam, dan bata son abinda zai taba mata farin cikinta ko menene Da mamaki Salima ta sake kallonta, to wannan tun yaushe rabintada fit? ko tace anya mutun ce kuwa? to ko aljanna ce ai tana iya gane an yi rasuwa abinda yan wani gari ma suka ji suka zo? ikon Allah Ajiyar ta sauke ta ce" To Ni kam ban gane ki ba, ki yi hakuri, ama rasuwar nan tun jiya aka yi ta fa, kuma mijin RAUDA ne ya rasu, kowa yana wajen Mah fa, kuma ace wani da yake cikin gidan nan bai sani ba?" Baki ta tabe, tana yarfe hannunta , itama fa tana ba Salima amsa ne dan ko daga skin dinta ta san ba yaku bayi bace A gafarance ta ce" Baki sanni ba? Ni ce matar HR EXCELENCY , I'M AMNAH!" Sai da Salima ya sake kallonta da sauri, dan abin ya shige mata kunne kai tsaye ne kai ta dauke, cike da mamakin wai da gaske ko a'a?, sai dai tunawa da ta yi y'ar Wacece, kawar mamanta sai ta yarda, ama abinda ya bata mamaki dama a nan aka dauketa? ai ita ta yi tunanin tana bangaren yayansu, kuma wannan abin da ya faru ba wanda ya tuna da ita, ikon Allah sai ta kasa tafiya har ta bude yar akwatinta ta ciro wata riga irin masu bin jikin nan ba ruwanta ta tube a nan ta saka bayan ta saka breziya da pant Salima ta dago kanta jin tana fesa turare, da kula ta ce" Aya, ban gane ki ba ai, inai maki oyoyo, ki saka hijabinki mu je wajen Mah din, a cen ne ake zaman rasuwar, mijin RAUDA ne ya rasu kanwar Malik ce!" Har ga Allah idan aka kirayi sunnan Mah sai ta ji gabanta ya fadi, ko dan an gama fada mata Mah din nan tsaf take iya hannata zama da mijinta ne? mtssss ita dai sam bata son ko sunnan matar, ama kuma sai ta shiga neman hijabin da ta amsa na maman Salima ta dauka ta saka ta dauki tanfatsetsiyar wayarta tana kunna wa dan tun cikin dare da ta gaji da kallon Tiktok ta kashe ta yar barci ya yi awon gaba da ita sai tashin nan da ta yi, bata nemi sallah ba, ko bata yi ne? bata dai yin ba yanzun Salima haka kawai take gannin kamar AMNAH din nan bata da kamun kai, kuma faratunan dake hannayenta hade da kunshi sun bata mamaki matuka, ama kuma akoy fari, farinta har wani yellow yake yi, kuma idan tana magana idannuwanta a tsaitsaye suke, hakama yannayin maganarta ita kam sai take gannin kamar irin mutanen nan yan duniya haka, ama kuma ba zata yanke mata hukunci haka ba, ta girmamata a matsayinta Na matar ƴaƴanta, ta yi mata jagora sun tafi a mutunce har bangaren Mah, a lokacin Hajia na tausar RAUDA kan maganar cin abinci, firr RAUDA ta ki ta ci komai, ga kuka, ga jikinta zafi, hakan na neman birkita lissafin Mah da duk wani mai kaunarta, domin tunda aka saka ta saka wani katon hijab aka bata carbi aka tabatar mata daga jiya ta dauki nadin amarci a kanta yau na takaba ya kamata, wata hudu cif da kwana goma a duniya, du sai ta sake rikicewa har suka shigo tare , Salimar ta kai wayar wajen Mamanta dake zaune tare da dayar abokiyar zamanta, sannan ta wuce ciki inda Hajia ta shige da RAUDA, wato dakin Mah, hakan ya sa mahaifiyarta rakata da harara a ranta tana jin in sha Allah wannan karron idan ta rike Salima sai ta yi mata tsinanan dukan da zai dawo da ita hayacinta, dan ta kula kyaleta da take yi ne take son fin karfin ta Zaunar da RAUDA Hajia ta yi bakin gadon nan, ta amshi madara mai dumi da Mah ta kada mata tana kallonta ta ce" Maza sha kadan kadan, ba'a so idan ciki ba komai a ci abu da yawa kuma ba zai yiwu ki zauna da yinwa ba kin ji y'ar nan? yaya zamu yi? Allah ne fa ya amshi abinsa, idan kika yi haka ai baki godewa Allah ba, ki yi hakuri kin ji? mutuwar nan muma ita muke jira, Allah ya kyauta namu zuwan" Mah ta amsa da amen , ta mikawa Atu kwanon abincin ta nufi wayar dake dakinta tana kukan neman agaji wayar ta daga a nutse ta yi salama YUSUF dake zaune a falonsa tare da baki a nutse ya ce" Barka da warhaka Mah, yaya hakuri" Mah ta amsa a hankali sannan ta yi shiru tana sauraronsa A nutse ya ce" Akoy daidaikun mutane dake zuwa da maganar bashi, na kansa da wanda yake bi" Mah ta bude idannuwanta dake dan sade, a hankali ta furta" Aya, ka ga kuwa a jiya Allah bai bashi ikon yi min maganar nan ba, ga fa akwatin da ya bani ban sani ba, ko abinda ya yanke haka din ne, ita daya ce zata gaje shi ko yayane, ga dai takardu na dukiyoyi da kys din gidajen da na motoci da kuma harkar banki, bashin da ake binsa ai ko nawa ne kawai a fadi sai a biya ko?" Dan shiru ya yi, sannan ya furta" Na biya , wa'inda aka kawo kuma gasu ajiye" Mah ta ringa godiya, har sai da ya ji kamar yace ya isa ama ya san in ya fada din ma sai ta ga dama zata bari "Salima yi maza jiko min tawul na goge mata jikin haka, barshi shan madarar ya isa haka" Muryar Hajia ta shiga kunnayensa A hankali ya dan daga idannuwansa a lokacin da Mah ke fadin" Ina Amnah ne? " Har ga Allah sai ya rasa wace Amnah, sai da ya ji Salima na fadin" Tana falo wajen su Mama " sannan ya dan yi shiru ya tuna ashe wannan mai kama da birin ce Amnah Shi kam sai ya yiwa Mah salama ya ci gaba da hulɗar dake gabansa A cen wajen Mah kuwa sunna samu Rauda ta dan daidaitu suka fito falon Mah karami, a nan Mah din ke sanarwa Hajia abinda ya faru a jiyan sosai Hajia ta sha mamaki, Bama kamar maganar dukiyar nan, sai ta rasa abin fada, sai adu'ar da ta ringa binsa da ita ta saka Mah ta kai akwatin ta adana tace sai Malik ya nutsu a kai masa abinda ya yanke sai a yi Mah dai ta adana ama ba Malik zata kaiwa ba gaskiya, Bah zata ba ya ga uncle dinta abinda suka yanke shikenan. Dare na tsalawa MALIK ya gama salolin da ya saba ya haye saman gadonsa dake gyare fes fes ya shiga kiran SHAHEED a waya yana tunanin ta yiwu yana cen yana barci ko yana ibada "kai, me kake yi nake ta kira baka daga ba, hala har ka abin an ?" SHAHEED ya fada a tausashe bayan ya bude idannuwansa da suka yi masa nauyi sosai dan barci ya fara sandarsa Kai ya girgiza ya ki bashi amsar tambayar tasa sai wata tambayar da ya yi masa yana dubansa ya ce" kai, wai kiran nan na meye? ina NAJEEBA" "Ciki na dirka mata, tana cen tana yan amaye amayenta, na so zuwa suturar wannan bawan Allah, sai dai ban samu zuwa ba, ama in tambayeka ba shine mijin RAUDA ba?" Da sauri YUSUF ya bude idannuwansa ya yi shiru ya kasa cewa komai sai da shaheed ya ce" Ikon Allah, bawan Allah ashe lokacinsa ya yi, Allah ya masa rahama, dama ba matarsa bace ita, taka ce" Idannuwan nasa ya kai kan wayar, yana jin wani tukuki na tukarsa kai ya girgiza a hankali yana maida idannuwansa yadda suke, kasa kasa ya ce" Bana tunanin zan iya , Ni ba namijin da za'a ringa wulakantarwa bane, man sumanta biyu , kuma inaga yanzuma bata da lafiya, in ba raini ba ai binsa take sai na idasa yarda da soyaya......Please daina min maganarta, dan ba zan taba yafe mata ba, yi min maganar dawakan nan da nace maka muna da Muradi!" 🤔🤔🤔🤔🤔 Biya Muradi kamar kana son zuwar mana da bidia koda yake zamu ga waye zai cika maganarsa shin zata damekan ne, ko ba zaka yafe matan ba? a ringa yi ana karbar BONANZA 🥹, a 1k in sha Allah gaba daya LITATAFAINA, a TUNTUBENI BISA NUMBANA KAMAR HAKA 93811618 Azl 44 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo Sosai Shaheed ya yi murmushin maganarsa, shi dinma ya ki nacewa kan maganar, a ransa ya kudurta zasu yi maganar ne, ama shima in sha Allah sai ya ja ransa, abu daya ya san ya yiwa kansa alkawari, in dai ya sako ƙafarsa da nufin zuwa gaisuwar rasuwar nan ba zai fitar da kafar tasa ba sai ya ga Hajia, gannin Hajiar kuwa mai lasisi zai yi, dan kuwa a zamansa da YUSUF yana iya cewa a kusa kusan nan da wahala wani ya fada masa halinsa, walahi tsaf zai iya sake nuna taurin kai a lamarin, ama idan har manya suka ji, walau su karra kusantata da shi ta yadda ko ya ki ko ya so zai zubar da makamansa ya nemi sulhu, ko su tayata yaglgala masa lissafi ya yadda lokaci daya zai yi saranda ya nemawa kansa mafita da kansa Maganar dawakan suka yi, yace su Taj zasu je su gani su zabi adadin da ake so sai a yi transfer, dan harkar kasuwanci ce, dawakai kuwa kowa ya sani sai a gidan kiwon mai Damagaran! Washe garin ma haka aka yi wunin zaman makokin Sosai Mah ke kula da RAUDA, hakama Hajia dan ita ke tirsasata cin abinci Atu kuwa tunda safe take zuwa sai magariba ake zuwa daukarta Salima kam tana nan tare da ita, duk irin dakon da mahaifiyarta ke yi dan ta damketa Allah bai bata dama ba har yanzu ta wani gefen kuwa Mah wani abu na matukar bata mamaki da dukan zuciya Ba komai bane sai irin yadda take hankalce da lamarin amaryar YUSUF! Bata taba gane cewar ba a bangarensa take kwana ba sai da aka yi kwana na hudu ana zaman makokin nan, shima a ranar iyayenta suka zo gaisuwa ta ji sunna maganar ya dace a san inda take zaune dan a kai suturunta gaba daya domin ba zai yiwu a kai bangaren Hajia ba Sai a nan ta gane wai a bangaren Maman Salima take kwana duk tsayin lokacin nan Ba wai kwananta a cen ta ga laifi ba, a'a, maman Salima ai uwa ce a wajen YUSUF, haka kawai dai take dan fuskantar yarinyar kamar da wata a kasa bale tunda take zuwa wajen zaman makokin nan bata taɓa zuwa tunda sassafe ba, wani bin har sai an yi sallar la'asar take zuwa, kuma idan ta zo takan samu kujera inda ba zata takura ba ta yi kwonciyarta tana dana wayarta, ba'a taba tashi dan a bayar da abinci ta tashi ta taya raba abinci ba, ba'a taba kokarin yin wani aiki ta mike aka yi da ita ba, kai ko yannayin yadda ta kula tana kallonta lokaci zuwa lokaci sai abin ya dan dameta, dan ita da ita dai gaisuwar kirki irin ta daban din nan ta sirikinka bata hada su ba, domin in zata gaisheta a takaice take ce da ita morning Mah, shikenan abinda ke shiga tsakaninsu, shi dinma tsaf take gane kamar waje ke kure masu shi yasa take yi mata shi? Ita dai lamarin na son damunta, sai kuma ta ga tsagar idannuwan uwar da yayarta, sosai ta gane kamar an shiga gidan kosasu kuma isasun kansu halaya, sai ta ji hankalinta zai tashi Ita a rayuwa ta san bata taba raina Hajia ba, kai ko abokanan zamanta sai da rayuwa ta yi rayuwa tafiya ta yi tafiya ta yi hakuri da son dole sai sun fahimci junna ta kawo ido ta zuba masu take sha'anin ta ba tare da ta tsaya sun yi mata ba ,ko wanin abin ya haɗa su ba, haka A'isha sai da ta ga irin yadda take zaune da ita fa da gaske take ba zata kiyaye hakokin zaman tare ba sai kawai ta yanke hukuncin tsakaninta da ita gaisuwa idan ya kama dole, dan a shekaru ta girmi A'isha ba zata tsaya ta wulakantata a banza da wofi ba, haka kurum sai take gannin kusancin bai yi dankon da zata sauka cen ba, ama kuma ta karra yin shiru aka ci gaba da zaman makokin nan har aka yi sati Daya, aka yi na biyu, aka aka zo ake maganar arba'in ya zamo daga baya ko a leke bata lekowa , itama ta share ta yi kamar bata nan, dan a yanzu walahi wanda zai ci gaba da bata wahala mutun daya ne tak, Hajia baba, itama dan uwa ce, ta haifa mata miji, ta isa da ita, kuma ta isa ta gana mata dukkan azabar da ta yi niya, kuma ta yafe mata dan ko Tata uwar ce ke yi mata haka ba zata taba riketa a rai ba, sai dai ta yi mata fatan Allah ya sa kafin ta koma ga Allah ta daina , dan Allah ne ya halice su baki daya, ko me ta aikata a rayuwa shine zai hukunta ta ba wani ba. Gaba daya sai ta maida hankali kan RAUDA, da su Atu, da yan uwanta wa'inda ke kai kawo, sosai ta basu damar su ta sake masu fuska ainun, ama tsakaninta da su ba maganar auren YUSUF bale abinda ya shafi sirrin zamanta da mijinta ko da dangin mijinta, wanzuwarsu a tare da ita din ya yi anfani sosai dan komai sunne a tsaye a kai , domin ita da kanta ta gane zaman da matan Bah ke yi saboda Hajia na kusa ne, kuma a haka din ma idan suka zauna sai su yi clan din su sunna shan firarsu da dariya da komai, shi yasa ta kauratar da RAUDA ciki gaba daya da zama, bata yarda wani ya tardata ko ita ta fito haka ranta ya kiya, komi ciki ake kai mata har sai kowa ya watse sannan ta fito ya rawata a falo saboda zaman waje daya, gashi zaman nan da take yi a daki cikin ac ba aikin fari ba baki, duda zaman rashin mijinta ne yannayinta ya karra daukan zafi, domin idan ka kalli RAUDA tsaf zata birgeka, tana nan da yannayin mutun mai sanyi a ido, ama idan ta budi baki ko wani abin ya bata haushi tsaf zaka ga akasin hakan, Balle yanzu da take cikin wannan yannayin, sabon hali ta dauka na rashin surutu da wani irin sabon salon bada amsa wa magana, domin idan har ya zamo dole ta yi maganar ne take yi, dan kuwa a yanzu take baby, ko dan ta ga ana shagwabata ta hanyoyi daban daban sai ya zamo baya ce mata komai ta dora kanta a saman Hajia baba ta fashe da kuka, Hajia baba fa jama'a, dan kuwa yiwa Mah dinta rigima abu ne da ya gama zama a jinin jikinta, ko Abdul karami sai ya fashe da dariya idan ya ga ta turo baki ana cewa ta ci abinci ta kiya, Fatar jikinta kuwa ta zama tamkar kwai, dama ita ba wai fara ce kal kal kal ba, ama tana da hasken fata sosai sai kuma ta hadu da hutu, hakan ya sa fatar ke sheki ko bata yi wanka ba, ta rame gaskiya, dan sosai cin abincinta da tunaninta sun yi yawa, ama kuma ramar bata lalata kyan da ta yi ba haka rayuwa ta yi ta tafiya, Mah na rayuwarta da ƴaƴanta a bangarenta, kuma tunda aka yi rasuwar RAUDA ke takaba a bangarenta Bah baya zuwa dan ziyarar kwana sai dai Mah din ta tafi idan ta tabatar da sun yi barci ita da Salima, domin Salima a nan take kwana tunda abin ya faru, karshema su dai sun ji Bah ya kirayi Salimar da Mah ya basu umarnin ta maido kayanta nan da zama , zai ga in wani ya haifa masa ita! Ita dai Mah bata da ta cewa, tsakaninta da Salima haihuwa ce dan yarinyar ta maidata uwa, itama kuma ta yarda y'arta ce, duk wani take taken mahaifiyar Salimar kamar ana zubawa a bayan kwarya ce, dan sarai tana hankalce da ita wuri take nema ta samu ta fake yadda zata yiwa Salimar ama abu ya gagara dan Salimar ta ki yarda su kebance daga ita sai ita, Abdul karami kuwa dama ya zama ɗan daki uku, watarana ya kwana wajen Mah, wataran ya bi Bah bale idan yace masa ya zo su je su ci dadi, wataran kuwa ya kwana wajen mahaifinsa domin har yanzu Abah ya ki tafiya, burinsa ya ga ta gama takabar nan sai ya tafi, dan ko da mahaifiyar Abdul da inna suka ringa zuwa wai mahaifiyar Abdul din mijinta ya saketa saboda tunda suka yi aure ta haifa masa mata sau biyu, shine yace ba zai iya ba shi maza yake so dan bakin ciki ai tsohon mijinta namiji ta haifa masa shine shi zata haifawa mace ya salameta ta dawowarta take yan toye toyenta da idarta hankali kwonce , to sukan zo idan sun sha kwana wajen RAUDA da Abdul din, itama sai da ta yi ta yi da shi ya tafi RAUDA yanzu ai ba ita kadai take ba, yace zai tafi, ba wai ya raina abinda ake yiwa RAUDA bane, ba kuma yana nufin shi ya isa ya bata farin cikin da ya fi wannan bane, yana so ne ya kasance da ita , shi dai yana so ya zamo shima tare da ita har ta fita takaba sannan ya tafiyarsa , shi yasa a kulun ta Allah sai ya zo bangaren Mah a ƙafarsa ya tsaya a falon farko da yama ko da magariba tare da Abdul ta fito sun gaisa ya tambayeta tana lafiya ta tabbatar masa sannan ya koma nasa bangaren, a ƙafarsa duk irin nisan gurin, wanda itama hakan ya matukar kara kusantata da shi , hankalinta ya karra kwonci da yarda cewar yanzu kam ya bar abinda ke fitar da bawa daga cikin duniyar tunani ya kai shi ta maye. Yau tunda sassafe, tana gama Sallah zata shiga tatare gadon da ta kwana sama Mah da ta fita saboda kiran da aka yi mata tun kafin a shiga masalaci ta dawo da kula ta umarce ta kan ta yi wanka ta fitar mata wasu hijab masu tsararan kyau ama kuma rufafu har kasa ta ce ta saka zasu je bangaren Hajia ne ana kiransu Hankali ta maida ta kimtsa din, ta saka farar Safa, Tuni Mah ta gyara gadon dan haka ta je saman kujera dan ta dan shafa mai kadan idannuwanta na kallon kasa tana irgawa cewar yanzu fa ABDALLAH ya kai wata hudu da kwana uku cirrrr da rasuwa, abinda ya rage mata a takabar da take yi kwana bakwai ce, hakan ya sakata dafe haba cike da mamakin rayuwa, kwonci tashi yanzu irin yadda kwanaki ke gudu dan Adam baya ganewa sai ya ji guri ya kure lokaci ya yi ba damar kara koda minti ɗaya ne zai gane ashe duniyar na gudu "BABY?, tashi mu je" Mah ta fada bayan ta leko dakin tana gyara zaman hijab dinta MUN SAKA BONANZA TA NOVELS DINA A KAN FARASHI MAI RAHUSA IN SHA ALLAH, 1K NE KACAL HAJIATA SU 22, KI TUNTUBENI BISA NUMBANA KAMAR HAKA 93811618 THANK YOU 😍😍😍😍😍 Mikewa RAUDA ta yi da sauri ta dauki kan karamin carbinta fari kal irin na sarkafawa a yar yatsar nan ta sarkafa ta dauko zug din maganin Mah na Hausa na ciwon kafa wanda take sha kodz yaushe, shi yasa Rauda bata nisa da shi, kowani lokaci yana kusanta da zarar Mah din ta gilma sai ta zuba mata a dan kofi, dan mai maganin yace ya zamo ta sha shi tsayin sati biyu sosai, tana iya shan ruwa bayanshi dan shi din ba wani da yawa bane ake shan nasa Sunna daf da shiga, dan ta baya suka bi, wayar Mah ya dauki ringin, hakan ya sa ta yi murmushi dan ta tabata an taru su kadai ake jira, dan aiki ne ya tsayar da ita, kuma sai da ta dauki akwatin nan mai dauke da takardun RAUDA ta kai sannan ta kirawo ta, kuma ko a lokacin da ta kai Bah din na nan da Aba da kuma Hajia, ta yiwu MALIK din ya karaso shima A nutse Mah ta fara shiga da salama a bakinta, RAUDA na biye da ita a baya itama ta yi salamar kasa kasa tana dago dubanta dan gaisar da mutanen dake falon, a lokacin ne kuma daga Hajia har Bah ke fadin" Baby kin tashi? Hajia kuwa na fadin" Zo nan autaliya taho nan zauna" Aba umar kuwa yana murmushi ya sada kansa ɗan a duniya bai san da irin abinda zai iya sakawa mutanen nan ba, ya san bashi da abin basu, sai dai adu'a, shi yasa ya sakawa kansa duk in dai zai yi sallah to sai ya yiwa daya bayan daya adu'a ta alkhairi A zaunen da yake, bai dago dubansa ba, ama tunda muryarta ta furta Barka da safiya Hajia, Barka da safiya.........da irin sunnayen da Hajia da Bah suka kirayeta da shi ya saka shi jin wani abu mai kama da haushi haushi da mamakin Hajia, dan kuwa bai taba tunanin akoy mutumen da zata so bayanshi a duniya ba, sai kawai ya dan dago da dubansa dan kallon Hajiar, sai idannuwansa suka sauka a kanta a lokacin da ta karasa ya zauna daf da Hajia, ta kare da dora kanta a saman cinyar Hajiar abinda shi bai sani ba, kuma bai taba gani ba kennan, shi yasa ya kalli Mah da sauri da kuma mamaki ya ga Mah din shi take kallo tana murmushi, dan haka ya dan tabe baki kadan yana duban Mah da kyau ya furta" Barka da safia MAH" Mah ta karasa ta zauna domin da shi kadai ne basu gaisa ba tana dubansa ta amsa da kula sannan ta masa tambayar gajiya, shima ya amsa din Sai da aka nutsu da gaishe gaishen junnan cikin dabara RAUDA ta silale kasa ta yi zaune daf da kafar Hajia, kanta a kasa a lokacin da Hajia ta yi hamdallah tana dubansu ta ce" Sati biyu da suka wuce na so mu yi zaman nan, sai Bello yace a yi hakuri har ya cika wata hudu da rasuwa sai a yi maganar, shi yasa na dakatar" Da dan mamaki YUSUF ya kalli Hajia, ikon Allah yanzu kennan har ya yi wata hudu? hakane fa, dan kuwa ya zarce hudun ma Hajia ta dora da fadin" Dangane da dukiyar matarsa ne, nace a zauna a san matsaya, Ni dai ida so ko menene aka yanke ta koma makarantar ta, ta islamiyya da ta boko, kafin Allah ya fido mata da wani mijin, kamar yadda na maku bayani kafin su karaso kuma akwatin ke gabanku da kuma na wajen MALIK duka da aka hade gasunnan, Malik ya nuna cewar Uncle dinta ke da wannan ikon, shi zai adana mata dukiyarta, nima kuma na yarda, gatanan dai a gabanta dan ta san komai ya sa nace a zo min da ita " Hajia ta ajiye maganar, Mah da Bah sunna gyada kai alamun hakan ya yi, sai dai shi uncle Umar kansa a kasa yake dai da suka saurara ya dago yana neman damar yin magana, hakan ya sa suka bashi dama A tausashe sosai ya ce" Ku yi hakuri, ku yi hakuri, ku yi hakuri, ama Ni ba wanda ya dace da rikon dukiya irin wannan bace, san kuwa Ni tsoroma kudaden nan da gidajen nan suka bani, Dan Allah a yi hakuri ama babu wanda ya cencenci ajiyar dukiyar nan sama da HONORABLE ko MALIK, a yi hakuri kar a hadani da rikicin nan dan tsaf barci zai kaurace min " Ya karashe maganar da raha, wace Hajia kadai ta yi yar dariya Bah shima ya sauke ajiyar zuciya yana dubansu ya ce" Ka san dukiya irin wannan, ajiyar ta ba abu ne mai sauki ba, a wannan zamanin da duniya ta ki gaskiya ko bankin ka kai sai ya zamo ka san me ake ciki me ke shiga yake fita, saboda yanzu duniya ta ki gaskiya sai hamdallah, dukiyar nan in dai ba wata damuwa a sakata a hannun YUSUF , shine zai sakata inda ya dace" YUSUF kam du sauraronsu yake, bayanan su na saka shi nazartar lamarin har sai da suka gama magana ana ta fadin eh shi zai adana, kanta a kasa ita, shi kuwa yana bin su da kallo sannan ya dan sauke ajiyar zuciya a nutse ya ce" Babu wanda zai ajiye mata dukiyarta sai ita da kanta!" Gaba dayansu sai da suka dubi fuskarsa, shi kuwa a lokacin da ya ajiye maganar ya dubeta ne, hakan ya sa suka yi ido hudu shi da ita Kansa ya dauke daga dubanta ya maida kan Hajia, Mah, da su Bah ya ce" Da ace sun haihu, dole za'a yi rabin gado a killace na abinda suka samu har zuwa yadda Allah ya yi, ama a yanzu dukiyar nan tata ce, kuma kudi ne da gidaje, ba zai yiwu a killace su a ajiye har zuwa yaushe? kudi juya su ake yi, saboda komai yawansu idan ba'a juyawa sunna iya zama kadan, gidaje za'a saka mutanen da suka sani su bi daya bayan daya, wa'inda suka zamo ba zasu anfanu yadda ya dace ba za'a saida a gina wasu ko a sayi wasu ginanu, wa'inda zasu anfanu za'a ba manyan ma'aikata haya, ta yadda kudi zasu ringa shigowa a duk lokacin da ya dace kuma in zasu bar gida zasu gyara dukan abinda suka lalata" Ya dan dakata a nutse ya dora da fadin" Dukiya da ta zama ta kudi za'a yi dogon tunani na abinda za'a dora na kasuwanci, a taba kadan ba da yawa ba a gwada, ta kula da abinta da kanta, ba ina nufin ta je ta tsare ba, daga gida komai ya shiga ya fita tana gani tana kuma bi har a ga abinda ya bada, idan har ya je yadda ake so sai a sake daukan wata hanyar ta yadda kudade zasu ringa shigowa ne yadda ya kamata" Ya sake dakatarwa da maganar da yake yi, sannan ya dora da fadin" Zai zamo da account daban wanda kudaden kashewarta na abinda ta yi niya ne a ciki, domin rayuwa ce, tana iya son yin wata gwaninta Tata da mutanenta, kuma idan ya zamo tana jin nauyin tambayar mamanta sai kawai ta yi abinta kai tsaye, ama na haramta mata ciyar da kanta ko tufatar da kanta ko yiwa kanta wata hidimar da aljihunta in dai ina ray..." ya dan dakatar a hankali ya furta" Raye....." Ya sake dubansu, dan irin yadda fuskokinsu suka yi, ciki harda ita da ta kasa daina kallonsa, dan ko ta dauke idannuwanta sai ta maida kan fuskarsa a nutse ya furta" Babu abinda zata yi da kanta, ama dukkan abinda za'a yi tana wajen da kuma izinin ta, Abubuwan ajiyewa za'a bude wajen ajiya, na rikewa a gida za'a ba Mamanta ta rike mata, Allah ya bamu ikon kiyaye hakin wani" Kusan gaba daya da amen aka amsa, Hajia kuwa ta wani gyara zama tana murmushi ta ce" gagara kake uban marayu, gagara kake uban talakawa, ja gaba kake uban masu uba, mararsa ubanma kai ne babansu, ka yi naka ka yi nasu ka yi na masu karfi , na mararsa karfinma kai ke yi, Jikan Hajia khadija kake, jika a wajen gagara marigayi d'an Bello da Ameerah ikon Allah...... Dole...." Kallon da ya dakata yana mata dan niyarsa tafiya saboda yanada abubuwan yi sosai, ama ikon Allah na Hajia ya saka shi yin turus yana kallonta ya sakata dan tsagaitaWa , ama bata yi shiru ba sai da ta kalli Bah ta ce" Yanzu yaya ka ga abinda na fada maka a lokacin da nace maka tabas yadda ka fada MAKIK , MALIK ne?" Kai ya girgiza kawai a tausashe ya ce" Shikenan? in tafi?" Kafin Hajia ta yi magana Mah dake murmushin Hajia ta dago da kula ta ce" AA, kar ka tafi, ina son sannin ina matarka? yaya aka yi wata hudu kennan da aure bata hau abinda ya dace ace ta hau na darajar dake kanta ba?" A tausashe ta fada, sai dai kana kallo zaka gane abinda ta tambaya amsarsa take so, RAUDA, kanta ke kasa, a hankali ta samu kanta da jin sarawar kai , a hankali ta lumshe idannuwanta ta ki dagowa , dukda ta so mikewa ta bada waje, ama kuma ta kasa hakan dan haka kawai ta ji dole sai ta ji amsar nan! Hajia ce ta dauki magana tana mikewa ta ce" Ya Salam, wai dama bata bangarenki yarinyar nan? da bakina na ce da ita bangarenki akace ta je ba na Hajia ba, Ina zuwa" Ficewa ta yi, Mah kuwa ta dauke dubanta daga fuskar Bah, tana kallon gefe daya, a ranta tana ayana' Ba fa zai yiwu ba, sai dai na ringa tsintar wasu abubuwa dake iya zubar da kimar dana a banza a wofi? a zuwanta gidan nan, ma'aikata uku ta kora dan jin dadi da isa, a cikinsu harda wace tun kafin a haifi YUSUF din take gidan, wai aikin me zata yi ta tsufa ta yi tafiyarta, sai ita ta saka aka maidata bangarenta, dama ba wani aiki ne take yi ba, tana dai dan abubuwan da ana zasu gagareta ba dan da aka nemi ta zauna ta huta ba zata rasa dukkan abinda ya dace na rayuwa ba, ta nuna dan Allah a barta ta yi aikinta dan idan ta zauna zaunewa zata yi . An dauki mintina kusan sha biyar Hajia ta shigo ranta bace tana tafe a hankali a hankali duba da jikin tsufa , ama muryarta radau tana fada ta dubi Bah dake zaune saman kujera ta kai zaune itama saman kujerar daidai Hajia ta shigo , bayanta kuwa Amaryar da ake nufin tasa ce ta shigo itama , wace shi gaba daya yake mantawa da ita, dan ya yi waje daya ya ajiyeta tuni, Hajia ta ce" BELLO, ya dace ka tsawatarwa iyalinka kan abubuwan da ake son sako min, wa'inda bana tunanin in zan iya hakurinsu, ita a wa zata kai AMNAH bangarenta ta zauna, ? inace nan MALIK yace ta zauna shine zata zaune tsayin watannin nan a bangarenta tana kallo bata zo ta sanar min ba? me kennan? hanyar da za'a saka yarinya ta raina min jika ake nema dan kuwa an saka ta baudewa umarninsa me ake nufi in ba haka ba? a'a fa, Ni dama na so a duba lamarin nan aka dakatar da Ni, bafa zan dauka ba!" Ta karashe rai a bace, shi kuwa ya ringa kallon Hajia da ta zauna tana sada kanta a nutse ta furta" Allah ya huci zuciyarki Hajia, ban san hakan zai haifar da matsala ba, kuma ban san baki san tana cen ba" Hajia baba ta ki bata amsa dan ita abin ya bata mata rai, kuma da ta je yanzu yarinyar nan barci take ta yi, a dakinta a saman gadonta, ita dai rabonsu da junna da iyayenta da suka yi maganar wai a kai kayanta bangarensa ta nuna a kawo bangarenta a ajiye wasu, wasu ta ajiye a na Mah din har ya yi magana, ta nuna bata so a kuma dawo mata kan maganar dan ba zata lamunta ba, idan aka matsa kuwa su je da ita kawai zasu waiwayo su, dan ita diris take jira a san yadda aka yi, dan ba zata taba so ace wannan ce matarsa ta farko ba, uwar yayansa, itama tarbiyya bata isheta ba bale ta ba wani! Bah ya saka baki sosai wajen ba hajia hakurin shima, dan a yanzu abinda zai iya yi kennan, dan a kashe maganar, ama shima zai ganta ta fada masa manufarta hakurin da Bah ke badawa kuwa sai ya kular da Mah, gani take yi ita da ta fada masa kennan bai yarda ba? gashi kuma da Hajia ta fada yana tarewa kar a yi magana ko? ba laifi su ci gaba da yi, ita dai akoy lokacin da ba zata dauki abubuwan nan ba! Uncle Umar kuwa gannin abin zai kacame sai ya yi kamar yana amsa waya ya fice a falon, yana son ya kirayi RAUDA ta basu waje itama, ama kuma ya ga kanta a kasa bata dago ba ko kadan, kuma ya sha mamakin gannin bata fita ba, ko me yasa? Da kyar Hajia baba ta yi hakurin, Hajia ta mike ta tafi, zuciyarta cike da farin cikin ko ba komai a irin turbar da ta karra dora yarinyar ko a yanzu da wahala su ji dadinta, kuma zata ci gaba dan walahi bakin rai bakin fama ita da ANDIYA, ba zata taba jin dadin sarakuwa ba! Bayan hajia ta nunawa Amnah wajen da ta zata zauna, ta zauna din sai bin kowa take yi da kallo kasa kasa , Hajiar ta ce" Ka yi hakuri da take abinda ka ce , kuma Ni ban san cewa har yanzu bata cen din ba" Sai a lokacin ya bude idannuwansa yana kallon rigimamiyar kakarsa, ita dai a yi rikici baya ce mata komai, a yi ta surutu kuwa haka ta fi so Girarakinsa ya dan hade ya maida dubansa kan Mah, sai dai maimakun ya kalli Mah a kanta idannuwansa suka sake sauka, bugun zuciyarsa ya karra cenzawa kafin ya dauke ya maida kan Mah A tausashe ya ce" I'm sorry Mah, Ni bata wajena, wajenki na ce ta zauna ai " Mah ta dube shi itama tana sake daukaka lamarin yarinyar nan, farce ne na kari har a kaffafuwanta, shin ita bata sallah ne? A nutse Mah ta ce" Me zai sa kace ta je wajena ta zauna? aure ne fa aka daura maku, kuma a wajen naka da bangare bangare har hudu kamar yadda ka sa aka yi, me zai hanna ta je nata ta yi zamanta? YUSUF matarka ce, tana da daraja da kima, ya dace ka kiyaye , idan wani abin kake son yi ba dole sai ka yi yadda duniya zata fahimci halin da take ciki ba, ta je bangarenta da masu aikinta ta yi rayuwarta, wata hudu da da kwana hudu ba wasa bane, Ni kam ta je cen din kawai itama ta gyara gidanta!" Da YUSUF, da AMNAH, da RAUDA gaba dayansu Mah suka zubawa ido, kowa da abinda ke ransa Yaya aka yi ya ga duban da take yiwa Mah? idannuwansa dake yawan kai shi wajen da baya son zuwa ne suka kai shi? shi dai ya samu bakinsa da furta" Shikenan, ta je" Sannan ya lumshe idannuwansa yana sake bude su ya kawo su kanta, a lokacin itama ta zuba masa duban da ta saka idannuwanta cikin nasa tarrr ba tare da ta janye ba Nasa idanun ya dauke yana hade fuskarsa ya mike yana kade rigar jikinsa dan kuwa zai nunawa duk wani mai kallonsama ya isa ya yin ne! ya juya hankali kwonce da nufin tafiya AMNAH da farin ciki ya lulubeta, da mamakin dama kawai daga ta ce masa ta je yana yarda tun sarak take zaune tana jiran tsamani?, babu yadda bata yi da shi ba kan ta je ya nuna zai nemeta, sai gashi a yan sekwani an ce ta tare a bangaren da take ta dako da burin ganninta ciki? Hankali kwonce ta mike din itama, burinta ta fita dogaran nan su fara zubewa tana daf da shi, kuma tunda dai an ce ta je ai yanzu ake nufi, bata cewa kowa komai ba ta nufi bin bayansa hankali kwonce, hakan ya sa RAUDA kasa rikewa, Rauda dai Rauda, a nutse ta sake dagowa tana binta da kallo tun daga sama har kasa a tausashe ta furta" KE?" 🙄😭😭😭🙄🙄🙄 Ni kam bana son rigima, ke kuma? matar a gaban mijinta? kai jama'a hana Rauda zaki koma hali ko?, a gaban sarakuwarta da kakar sarki zaki ce mata ke? ☹️☹️☹️☹️🥹🥹🥹 Ita bonanza din tamu a 1k ce, litafina 22 ciif, a TUNTUBENI BISA NUMBANA KAMAR HAKA 93811618 45 Azl 45 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo KE din da ta fada, ya shiga kunnen duk wani wanda ke falon, da kuma wanda ke baki-baki, ciki har da YUSUF wanda ya ja ya tsaya a lokacin da ya dan shige lungu kadan dan ficewa gaba daya daga falon, hakan ya sa basa ganin sa, sai AMNAH kawai ke ganin sa, wacce itama ta ja da sauri ta tsaya sannan ta dan juyo dan ta gane KE din da wa ake? ko wata ake yiwa magana haka? kuma babban abin da ya sa ta tsaya din kar aje wannan masifaffiyar kakar tasa ce ke kiranta da sunan ke ta ki amsawa ta janyowa kanta balaki, sai dai tana juyowa ta ga idanuwan wannan dake zaune a kanta tsai, hakama na su Hajia a kan RAUDA din. Da ido RAUDA ta mata alamun dawowa sannan a saman lebenta ta furta" ZO NAN!" Idanuwansa a kan fuskarta ne, kuma dukkan motsinta shi dai YUSUF sai dai ya sanarwa wani abin da take nufi ba dai wani ya sanar masa ba, hakan ya sa ya sake zuba mata ido da matsanancin mamakin me zata yi? haka su Mah sai suka yi kamar an dakatar da su da Remot duk da matsanancin son su tambayeta lafiya? Sai suka gaza yin magana daga Mah din har Hajia, har sai da wacce mamaki da tashin hankali suka sakata juyowa rai bace ta dawo inda budurwar nan ke zaune tana kallonta ido cikin ido ta ce" Da Ni kike?" RAUDA a zaune take saman cafet, bata tashi ba sai kafafuwanta da ta dan janye dan kar ta hau mata kafa da wannan arniyar kafar tata tana kallonta cikin ido kasa kasa ta fura" Eh " Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, wallahi sai AMNAH ta rasa kanta ne ya dau juwa ko idanuwanta ke son rufewa saboda bacin rai ita dai abin da ta gane shi ne, rai bace har ta manta sirikanta a wajen ta nuna Rauda sama-sama kamar yadda ta saba fada da mutane irin ta ta ce" Kin san ko Ni wacece zaki dube Ni ki ce min KE ZO NAN?, ki kalli jikina tun daga kaina har kafata ki fada min na maki kama da ajebo da zaki raina min hankali? Uban wa kike takama da shi a duniya da zaki dube Ni ki ce min Ke Zo Nan?" RAUDA ta lumshe idanuwanta, sarai ita tana tune da su Mah na wajen, kuma bakinta ne ya cuceta da ya yi mata kiran yarinyar nan da bai dace ace wani abu ya hada su ba ko da mijinta balle ita banza a banza! A saman lebenta, bayan ta dan kauda kanta barin da iya shi da Amnah suke ta furta" UBANKI ya tsaya mini!" Sai kuma ta juyo ta bude muryarta da kyau a lokacin da ta mike, kuma a lokacin ne AMNAH ta zarro ido, hakama shi ya zarro ido yana kallon ta, a bayyane RAUDA ta ce" Ni ban san ki ba, na ga ne kina saurin yin cen kuma kin ga ba hanyar da kowa ke bi ba ne!" Itama da ta fadi hakan ta ji abin wani iri balle wa'yanda ke sauraronta, kuma sai da ta fada ta gane ta yi rashin azanci domin koda bata san ta ba ta san bakuwa kai tsaye ba zata shigo nan ba, kai abinda yanzu yanzu aka gama maganarta? Sai kawai ta waske ta kalli Mah da ta yi suman zaune, Hajia kuwa tana tafa hannu ta ce" Ba ga irinta ba, wannan fa kanwar mijinki ce, ama bata sanki ba, gashi a rashin sani har tace maki Ke , wannan din ai bai dace ba, kina da wa'inda suka fi su ne? da zaki je ki tare a cen inace Salimar ma nan take da su, ke ki yiwa kan ki karatun ta nutsu kafin duniya ta maki, wannan fa itace mijinta ya rasu kwananan, kenan ko gaisuwa baki yi mata ba?" Sai kuma Hajia ta sauke ajiyar zuciya tana kallon yadda AMNAH ke kallonta, domin Rauda tuni ta juya ta bar mata wajen dan kanshin turarenta sam baya birgeta! Wannan karron Hajia ta sassauta murya tana kallonta ta ce" Wai da bin shi ne zaki yi Amnah?" AMNAH kam kallonta take yi, tunda ta ambaci Rauda kanwar mijinta ce kanta ya shiga a halin rudu bayan bacin ran da ta shaka mata, wallahi tana iya rantsewa cewar RAUDA ce mata ta yi ubanta, kuma ta kirata da ke, kuma ace kanwar mijinta? kodayake da ta matsawa maman Salima kan Wacece RAUDA duba da an ce shi daya ne d'an mamansa sai tace mata ta yiwu iya ta haifeta kuma ta yiwu ba ita ta haifeta ba, su dai ta ce masu y'arta ce, kuma irin yadda Honorable ma ke kiranta da baby Auta ta yiwu y'ar tasu ce babu wanda ya san da ita dai su tsakaninsu tunda abin kunya ai ba na kunya bane a wajen su! Tana jin Hajia, amma gaba daya tunaninta ta yadda zata kasance da yarinyar cen ne daga ita dai ita, dan wallahi sai ta nuna mata asalin me ake nufi da dan kwalta, domin sai ta nuna mata da sarautar gidan nasu ta fi ta iya shege, har ita tana matar MALIK, zata yiwa wannan kiran , kuma ta zageta? A tausashe Hajia ta ce" Zauna Amnah, zo nan zauna" A dole ta je ta zauna din, ita Kuwa RAUDA a lokacin ta zuba maganin Mah a dan kofinta ta mika mata, bakin nan a cune kamar zata fashe ama ita batama san a cikin yannayin fushi take ba, Mah din dai ke hankalce da ita, shi kuwa tunda Hajia ta fara fada ya yi gaba zuciyarsa da matsanancin mamakin y'ar cen, daga baya kuwa ya yi wuri ya ajiyeta a ransa yana ayyana' Mai hali da wahala ya daina halinsa, idan ka ganta kamar ba zata ciza dan yatsa in aka saka mata ba, bayan duk wani rashin ji a kanta ya kare, Allah shi kyauta, wai matata ta yiwa haka? oh!" A tausashe Hajia na dubanta ta ce" Bana son idan ina maki magana na ringa yi maki a haka, ko menene halinki wanda kike da a gidanku ya kamata ace kin fahimci yanzu fa dole ko daidaita wasu abubuwan, Amnah ke budurwa ce, auren farko aka yi maki, kuma aure mai darajan gaske, ke ko a idon mijin naki bakya tsoron ki rage daraja ne? yaya za'a yi ki ringa abubuwa kamar ba mace ba? mace fa an santa na da kamun kai da aji, ke ya kamata ya ringa rawar kafa idan ya ganki ko waye shi, ba wai ke ki ringa abubuwan nan ba, namiji fa idan ya rainaka shikenan, kuma kin ga idannuwa fa a kanki, bai dace ace ko wani lokaci aka daga ido ana iya ganninki ba, ina darajarki take? ke da ya dace ace ko Ni sai ta kama zan ga fuskarki? kina bangarenki kina mulki daidai gwargwado? haba dan Allah, yanzun da binshi zaki yi? ki duba fa ki ga jikinki, suturar nan ai ba wace ta dace ace kin bi bayanshi bane shi ya dauki wanka kamar zai je hawan sallah ke kuwa da wannan abin? ki yi anfani da damar ki ki tabatar da kin gyara zamanki da mijinki sannan ki so ahalinsa, ba kamar mahaifiyarsa, idan kika kiyaye abubuwan nan na tabatar maki mijinki zai so ki, zai mutunta ki kin ji?" A lokacin da Hajia ke yi mata nasiha , irin wace zata fisheta, ita wasu tunani take yi daban na abinda zai fisheta Kwarai kamar yadda Hajia tace ita din mai daraja ce hakane, kuma tunda ta zo gidan nan suka yi watsi da ita take dauke da haushinsu Babu ruwanta da wani umarni ya bada ta je bangaren mahaifiyarsa, babu ruwanta da wani rasuwa aka masu, ko menene ya dace ace sun bata kulawa ta daban da ta kowa, ama tsabar son kai suka ki yin hakan kuma yanzu ake son nuna mata fi'ili Idannuwanta kuwa a kai a kai sai sun sauka kan RAUDA, a bayane take dan dantse lebenta, a zuciyarta tana ayana' Lalle baki san wace Ni ba, dan na yi zaman watannn nan a gidanku ba yana nufin na zama sharar da zaki taka ba, ko Wacece ke zan binciko zan nuna maki Ni din Wacece, na tabata ko waye ubanki ba fin nawq kudi ya yi ba, kuma na tabata du rashin jin ki baki kai Ni ba, zan san dalilin da yasa kika zageni kafin na shake wuyanki har sai kin kusa barin duniya, walahi na amshi tayin masifar da kika min, ko Ni Ko ke!' (Uhum, a yi dai mu gani, wannan tashin tashina haka) Hajia a tausashe ta sake fadin" Ki yi zamanki a nan bar dare ya yi a raka ki a mutunce, yanzu zan sa a kwashe kayan ki a kai cen din a kimtsa maki, bai dace ace an ga shigarki da rana haka ba kin ji?" Kai ta gyada, a lokacin ita kuwa RAUDA ta lumshe nata idannuwan da suka yi mata wani irin nauyi Kasa kasa ta furta" Mah, zan je na yi girki" Mah ta sake dubanta, da kula ya ce" Baby zaki iya? Sai na ga kamar baki da lafiya?" RAUDA ya girgiza kanta a hankali ta dauki jug din maganin Mah ta mike kasa kasan itama ta furta" A'a Mah, i'm fine, sai kin zo" Daga nan ta juya ta fice a falon , zuciyarta a cinkushe, tana jan carbinta ta karasa bangaren Mah lokaci daya ta je wajen kujeru ta zauna tana dan yatsina fuskarta, hakan ya ba dimple din kusan idannuwanta damar lotsawa Da dan takaici ta fitar da numfashi kadan daga bakinta a hankali ta furta" Aikin banza marar tarbiyya, ki shigo ki tardo manyan mutane ki kasa gaishe da kowa, ana magana kina kada kafa a gaban iyayenmu, kuma ki ce zaki tafi baki gaishe su ba? Ni bana son rashin da'a waye sa'anta a nan? Sai wani firirita take yi da takamar an san ita Wacece? wace ke banda shara ajebo?, abu daya ya tsallake fuskarki daga hanuna Mah ce!, in ba dan wannan ba da na gwada maki Ni din wace da kika zagar min uba, wace ke kuwa banda mace marar aji, wai gidan aure ne aka kawo ki kina azarbabi haka? shirme wata nawa da auren kina nan kina shirme?, mtssssss auren naku da babu wanda ya dama?...." (Mu dai ya dame mu☹️) Sosai take fada a zaune har ta cinye lokacin da ita da ganta bata ankara ba sai da ta dago dan ganin time ta mike da sauri ta nufi kicin din tana tunanin abinda zata dafa, domin haka kawai take jin ita kanta ya shafe ma bata san me zata dafa bama! A cen inda ta baro su Mah,Hajia ta jima tana yiwa Amnah nasiha da nuna mata ya dace ko me ta nado a turminta ta gyara dakanta dan uwar mijinta uwa ce a gare ta kuma bata da wata wace ta fi ta Mah na zaune ne tana bin su da kallo, ama a ranta tunani ne kala kusan hudu ya hadu ya rarraba mata yannayi A lokacin da akace ta bi shi, da farko ya so dakatar da hakan, domin a yannayin da ya yiwa fuskarsa ta gane ya so ya hanna hakan, sai dai idannuwanta sun nuna mata wani abu, domin a lokacin ne ta ga ya kuma kallon Baby, bayan kallon da ya mata fiye a irga tunda ta zauna, kallon da ya bambanta da wanda yake yiwa SALIMA, kallon da ta fadawa Bah tun cen baya ya nuna mata ba komai bane kar su ce wani abin ne, tana hankalce da shi a lokacin da ya ga ta dago da sauri sai da ya yi murmushi sannan ya nuna su je!.....Hakan ya matukar daure mata kai Sai abu na biyu, abinda Baby ta yi! a zamanta da baby, zata iya cewa yarinya ce mai hankaltuwa da abu komai kankantarsa ko girmansa, ta kasance mai kwontar da hankalinta a kan komai, abu komai kankantarsa baya shige mata, ta yaya Baby zata dube su tace wai bata gane ana nufin Amnah ce matar YUSUF ba? me yake faruwa da Baby ne?, a irin abinda ta ga yau ta yi, zata iya rantsewa bata taɓa gannin ta yiwa ko bawan gidan nan ba, wani yannayi mai tafe da rigima da neman fitina da wani yannayi mai zafin da kuma alamun son fashewa da kuka?......Kar dai duk irin yadda ta ringa bin su da tambayar nan cewar kin amince da auren wane? ka amince da auren wance dan kawai su yi kokarin kwatanta mata da wani abu komai kankantarsa suka yi mursisi dan su raina mata wayo ne? .... Sai abu na uku, yannayin Hajia! Hajia uwa ce a wajenta hakan da ta sakawa ranta ya sa take zaune da ita duk rintsi a rayuwa ta sha wulakancin Hajia wanda kare ba zai dauka ba a yanzu yannayin nan da ta samu sabo yana so ya saka ta fito fili ta tambayeta sanyi take son yi a kanta dan ta sakankance ta yarda cewar itama mutun ce sai ta sake da ita ta sake masheta baiwar da bata da ubangida?, da ace Hajia zata dubeta a matsayin y'a da ta dora kanta a saman cinyarta ta yi mata kukan dake kirjinta na tsayin shekaru ko komai ya wuce a ranta, sai dai zuciyarta na cike da matsanancin tsoron kar baya ta dawo gaba a sakata yin faduwar tasar da ba zata iya gyaruwa ba! dayan abin kuwa yarinyar nan ce dake gabanta zaune Tun daga kan yarinyar har zuwa dan yatsar kafarta ta gama gane cewar yaronta ya samu daidai da zamaninsa kuma Allah ya hada shi da irin classs dinsa....., haka kawai take cike da kukan zuci, wanda zuciyarta ta fi bata amsa daya tak *ME KIKE TUNANI ANDIYA? KALAR ZAREN KALAR KAYAN, AI DAMA DA WAHALA ALLAH YA HADA ABINDA BA DAIDAI DA JUNNA BA, TA YIWU ITA DIN RAINONSA CE!* , walahi wannan kalamai su ke gigita mata duniya, kuma ta fada ta karra da babar murya domin ba zata iya yin mugun son kai fiye da kima ta yadda zata take abinda ke gabanta ba, Amnah, tana bata tsoro yannayin Amnah na firgita tunanin ta, bata san me yasa ba, ta dai san cewa ba bada kama ne ke gabanta ba, zahiri ne! Sunne abubuwan da suka hadu suka yi mata kwawanya a kwonyarta "AMEERAH, ki je bangaren ki da ita, dan bata da wani wajen da ya wuce cen, zan sa a kawo mata suturarta da ta dace da kaurarta, zan sa a je a kimtsa mata bangarenta yadda ya dace, idan aka yi sallar isha'i zan saka datijawan mu na arziki da kannen ta su hadu su raka ta, ki yi hakuri da abinda aka yi maki da farko, ina mai tabbatar maki na za'a maimaita ba, " Hajia ta ajiye maganar a nutse, sannan ta sake kallon Amnah dake zaune, kanta a sade, domin duk yadda ta so yi masu kiririta da bin su da ido cikin ido ya gagareta, kai abinda ke kai kawo a cikin zuciyarta ya fi komai yawa, dan haka sai kawai ta sada kanta tana tunanin abinda ke iya fitar da ita Da kuma Hajia ta ce" Kamar yadda na fada maki, in dai zaman lafiya kike so da mijinki, ki girmama mahaifiyarsa, duk d'an halak ai inaga zai girmama baba koda ba shi ya kawo shi duniya ba ko AMNAH?, ki girmama ta, zaki ji dadin ta fiye da kowa a gidan nan, dan kuwa Ni sheda ce , ki tashi ki bi ta" Hajia ta idashe zancen tana mata nuni A hankali Mah ta dago dubanta ta sauke a fuskar Hajia,zata iya cewa ta jima tana yin sharar shanyen nan, domin lokuta da dama koda bata so bakinta ya fada ba idan tana yin fada da bada misali zata yi misali da ita ne a matsayin a yi koyi da halayarta....., abinda ke kanta a yanzu yanzu shine Hajia ta kasa yafe mata abinda suka aikata ita da d'anta ne, da ace ta yafe mata, da ta dubeta tuni, da kuwa ta ji dadin rayuwa tare da ita A hankali ta mike saboda zaman da ta jima tana yi, ta dan rage tsayinta a tausashe ta furta" Allah ya saka da alkhairi Hajia, mun tafi" Hajia ta dubi Mah, zuciyarta na tsintsinkewa da lamarin sirikar Tata, lokuta da dama sai ta yi yunkurin yin wani gagarumin abin da zai shirya tsakaninsu sai ta rasa ta yaya? ta ina zata fara? bale a yanzu da YUSUF ke kan matsayin nan, takan yi tunanin idan har ta nuna wani abu daga ita din har sauran jama'ar zasu yi tunanin ɗan Yusuf ya zama sarki ne take neman sulhu da Mahaifiyarsa, ba zasu taba yi mata uzuri ba, a matsayinta Na uwar da tashin hankali ya sama rana tsaka a cikin kishiyoyi da miji da tarin makiya kan d'an da ya fi kowani yaro kokari da zafin nema a cikin y'ayanta, d'an da ita da kanta ta gama sakawa ranta cewar da izinin mai sama shine jagaban garinta, ya zo mata da gigitacen labarin da ya hargitsa tunaninta, ya kuma ja ya tsaya, ta ja ya ja , ta yi ta yi kan ya hakura da ita ya nuna gwara ya mutu da haka, duk irin tsatsauran matakin da ta dauka a kansa ya ki yin hakuri, karshema ya kamu da zazafan ciwon zuciyar da a yanzu haka emotion na dadi ko na wuya ke rikita masa lissafi har ya fita a hayacinsa ba? ba zata yi mata uzuri ta auna a kanta ba, ta tabata ko MAH sai ta fasarata , shi yasa take ta kai tubanta wajen Allah, dukda ta san cewar Allah baya yafe laifin da bawansa ya yiwa bawansa, sai idan bawan ya yafe, tana rokan sa ya bata hanyar da zata daidaita tsakaninta da *SARAKUWAR TA* ne. A tausashe Hajia na duban Mah ta ce" (RAUDA kin bar wajen gatanan tafe☹️) morning alll......, Azl 46 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo A tausashe Hajia na duban Mah ta ce" Allah ya hutar da Gajia Anmi MALIK" Kunya ta ji ta kama ta, ta sake sada kai ta yi murmushi sannan ta mike ta yi gaba a nutse tana dan daidaita tafiyarta dan bata so ta bar AMNAH nesa sosai da ita AMNAH kuwa, tana biye da ita ne idannuwanta na sake bushewa da tunanin dake cikin ranta, burinta daya ne kwal ya samu kanta ita kadai dan ta yi abinda zai bata damar Sannin Wacece yarinyar nan, domin ta daukarwa kanta alkawarin koda ace y'ar uwarsa ce jinni daya sai ta shayar da ita mamaki ta hanyar nuna mata kofa bata auri ƴaƴanta ba ita ba sa'ar yinta bace, bale ace tana auren MALIK! Tana tunanin nan suka karaso Mah ta bude ta shiga tana salama Amnah na biye da ita A lokacin Salima na falon Mah tana aiki da computarta, dan ta tarda RAUDA kicin ne su yi aikin tare sai ta same ta yau bata son magana, domin tana aikin ne ba tare da tana kula firar da take mata ba, shi yasa ta taho ta yi zaune abinta ta barta da yan kurumcinta Da kula Mah ke amsa gaisuwar da Salima ke yi mata, ta dan ja tana tunanin inda ya dace ta kai AMNAH, a cikin dakunnan wajen Ta so kaita dakin RAUDA, sai ta nufi dakin kusan na RAUDAR da ita a nutse ta saka ky din da Salima ta dauko mata a dakinta ta bude tana fadin" Bismillah, bari mu gani ko sai an sake gyara shi? na san dai ko jiya an yi gyare gyaren dakunnan dake rufe" Salima ta fara shiga, ita kuwa Amnah ta yi tsaye a waje, dan ba zata shiga ba sai an tabatar mata wajen clean ne dan gaskiya ba zata iya shaƙar kayan mura ba "Bismillah aunty Amnah" Salima ta fada bisa umarnin Mah shigowa ta yi tana bin dakin da kallo sannan ya sauke dubanta a kan Mah, kamar yadda ta saba kallon mahaifiyarta tsai cikin ido ba wani risinawa haka ta dubi Mah din,dan bata san ita hakan Bama wani abu ne dake iya sakawa a ga rashin tarbiyarka ba kallon baba cikin ido Da kula Mah ta ce" Ki zauna a nan , dukkan abin bukata za'a kawo maki, idan akoy wani abin da kike so ki sanarwa kannenki, ko ki sanar min, kina da bukatar kitso ko kunshi ne?......" Mah ta karashe tana sake duban kaffafuwan Amnah, dan da ace sun yi wani sabon da ya dace ta yi mata katsamandan a al'amuran ta, da tace da ita ki yanke faratunan nan ki tsaftace kanki ko dan sallar ki, sai dai a yanzu wannan yarinya mata take a wajen d'anta, matarma bakuwa, mai cike da abubuwan da suke boyayu a duniyarta Itama kunshin dake hannunta ta bi da kallo, wanda bai jima da aka yi mata shi ba, domin mahaifiyarta bata barinta neman komai ta rasa a gidan nan, duk wani abin da zata bukata za'a turo mata ne kai tsaye, Mamanta ta fada mata kar ta yarda a ga kazantarta komai kankantarta dan a haka za'a nemi a rainata kai ta girgiza tana sake duban Mah sannan ta nufi wajen bed din dakin ta zauna hankali kwonce, hakan ya sa Salima dan zarro ido tana kallonta , ita kuwa ba wani damuwa ta ce" A'a, bana son kunshi, ina dai son gyaran kai da mak'up" Mah ta yi dan murmushi sannan ta juya ta fice Tana fita Salima da ta gaza motsawa ta nufo ta da dan mamaki ta ce" Aunty Amnah, yaya zaki zo ki zauna tun Mah na nan tsaye a saman gado? har yanzu fa bakuwarta ce ke kuma hausawa sukan ce in dai da kunya y'ar halal har ta mutu tana jin kunyar sarakuwarta!" Itama da mamakin tana kallon Salima, dan zata iya cewa a duniyarta tana mamakin Salima ainun, tunda ta san y'ar kishiyar Mah din ce, kuma a gaskiya sukan dan yi fira idan ta kama bale ba laifi tana girmamata sosai, shi yasa itama take yinta, da kula ta ce" Kunya? to meye a ciki dan na zauna?" Salima ta dan dafe habarta, a nutse tana kallonta ta ce" Aunty Amnah, kar ki ce meye a ciki dan kin zauna, kin san ana girmama mahaifiyar miji, bale wannan din koda bata haifi mijinki ba ko a gari kika ganta zaki sada kai idan zaki yi mata magana Dan matar sarkin garinki ce fa, a irin yadda muke da girmama sarakuna tana da kima sosai a idannuwan duk wani mai mutunci fa" "Ya Allah, Salima wai meye na yi na rashin girmamata? zama? to ai Ni Ko ubana ke tsaye ina iya zaunawa normal ne bale wace bata haifeni ba, Ni walahi mamaki kike bani Salima, matar nan kamar ba kishiyar mamanki ba, kina kallo yadda ta maida maki uwa baya a cikin gida ama ke itace abar ki raba? in dan kudin d'anta ne kema ai yayanki ne ina gannin kina iya takama da kudinsa ko? walahi ki farka tun wuri, kishiyar uwa ba zata taba sonki ba!" Amnah ta fada tana hangen wace ke neman izinin shigowa Salima da ta yi mutuwar tsaye ce ta iya juyawa ta bada damar a shigo shigowa ta yi ta duka har kasa tana miko jakar Amnah sannan ta juya kanta a kasa, dan a yanzu a gidan nan idan akace an aikeka wajen gimbiya ka kama adu'ar Allah ya raba ka lafiya da ita kennan , dan abu kadan zaka yi ta saka ka a uku, ta janyo maka tashin hankalin da zai sa ka tsani kanka ka tsani zama a masarautar Jiki ba karfi Salima ta kawo mata jakar ta ajiye mata, tana dubanta a tausashe ta ce" Eh lalle ba ita ta haifeni ba, kuma matar mahaifina ce , sai dai Ni tunda nake da ita alkhairinta na sani ba sharinta ba, rayuwa na juyawa kala kala, na yi wayo tun daga yarinta, zan iya ce maki ban taba haduwa da abinda zai sa na ji ta daukeni kamar wadda bata haifa ba, kin san menene aunty Amnah? ita rayuwar kanta idan ya zamo ka sakawa ranka kowa na iya cutar maka shikenan, ka shiga uku, domin babu wanda zaka yarda da shi ko ka yi mu'amala da shi da zuciya daya, bale idan kai dai a rayuwa tunaninka za'a yi maka asiri ko an yi maka ne? to in sha Allah ka ginawa kanka mugun ramin da zai hannaka kwonciyar hankali........, Bana tare da Mah dan arzikin dake tare da ita, idan arzikin ne kamar yadda kika fada iya wanda ya zuba min a matsayina na kanwarsa ya isheni rayuwa, bale ban cika saka buri a raina ba, sai dai jinina ne shi, mahaifiyarsa kuma yawa ce Amnah....ki huta lafiya" Daga nan ta ajiye mata jakarta ta fice, tana jin gaba daya matar yayan nata na fice mata a rai, dan walahi tunda ta zo take son gane wace ita? ta gane wasu halayar ama bata gane wasu ba , a yanzu kam tana kukan wannan jigo da aka yiwa gidansu, dan bata tunanin in har ya isa a kirayeshi bango , ko kuwa uwa mabada mama! Tana fita itama ta ja dan siririn tsaki, kasa kasa ta furta" Dama yaya zaki yi ya kasa isarki? daga ke har uwarki abinda ke iya isarku abin siyan jakata ne, kuma fa ban ga laifin ki ba, kawai dai mamaki kike bani , ama kuma kina da wayo daidai misali tunda kika iya bin inda zaki ji zuma ziryan ba mai haɗe da shuga ba, sai dai dukanku zaku yi bayani ne, dan walahi walahi babu shegiyar da zata rabar min miji idan ya shiga hannuna, zan ci gaba da nuna masa ban san ciwon kaina ba har ya shiga hannun nawa, a nan ne zaku san *AZAL* ta shigo maku gida Rai bace ta ringa neman layin abokinta, abokin sharholiyarta, dan daudun nan wayar na fara ringin ya daga a lokacin yana restaurant dinsa, domin abinci yake yi na siyarwa, da kararamba ya kama kirari yana fadin" Barka da yamaci uwar dakina, amarya kike kuma uwar gida a gidan SARKI SULTAN MALIK YUSUF DAN BELLO, ke dama matar manya ce bale kin gama tabatar mana, ci uban kannanun kwari masu rike jakar jaka dari, ke ce uwar masu gida, ke ce uwar masu kudi ke ce......." "Habu!" Amnah ta katse shi, duda irin yadda take jin dadin yadda habu ke wasa ta, a yau sai ta ji batta bukata, ta fi son jin abinda take son ji Da yannayin bada umarni umarni ta ce" Ka hau whatsup zan turo maka hoton wata yarinya, ama ban sani ba a yadda na dauki hoton ko zaka gane ta?, ka dai hau ka gani na dauki hoton ne ranar da ake sadakar satin mijinta dan ina son Sannin Wacece a yau yau!" rigar dafe dafensa ya shiga kuncewa yana fadin" Yanzu kuwa" Dan yannayin muryarta ya sa ya gane akoy wata gwarama tare da uwar dakin nasa, shi kuwa ba zai yi sanya ba dan a duniya ita fa uwarta ne gatansa, sha nawa yake karyewa, su ke tada shi a nemansa na yau da kulun, Zama ya yi ya bude data sannan ya shiga wajen sakwaninta bude hoton ya yi, ya shiga zooming din hoton a ransa yana ayana' in dai ta kwana ta tashi a Tsatsunburum ba zata boye min ba, kai ko a Damagaran ne makociyar Tsatsunburum da wahala ta bace min' Zooming din hoton yake da mamakin Wacece dare dare a saman cinyar Hajia baba? Hajia wato kakar MALEEK, domin halayar Hajia babu wanda bai sani ba bako da dan gari, an san wace Hajia a fannin tsaurin halaya da kamewa da kin yin wasa da jikoki, an sani a duniya YUSUF kawai ke rikitata ya yi yadda ya so da ita, bayanshi babu wanda ya isa har baban shi Fuskar yake kallo yana karawa Hoton ya dauka ya turawa Nafeesa yana sake dan zarro idannuwansa da tunanin kai anya? kai a'a, ba haka bane ya yi katari Nafeesar na online, yana tuna mata ya dana mata voice note ya ce" Wannan kamar RAUDARIYA y'ar larabawa?" Nafeesa sai da gabanta ya fadi jin sunnan RAUDA, kawarta a da, ko tace kawar kawarta wace a yanzu bata fatan ko hanya daya su hada bale wani abin ya haɗa su, hoton ta sake kallo, ita dai bata gane Hajiar ba, ama kuma ta san cewa lamarin RAUDA a yanzu ya fi karfin ta tunda ta koma rayuwa gidan su Ogan oganta wanda yake sarki a yanzu ta san ita dai ta sai hange Voice note din ta danna itama ta sanar masa kwarai itace kasancewar ya fi son ya tura mata rikakakiyar sheda sai kawai ya sake danna wani voice din yana fadin" Dubata da kyau Nafee tamu , itace wanda ta yi maki shashawar nan? dubata da kyau fa" Nafeesa ta maida masa amsar cewar itace ko mutuwa ta yi ta dawo na zata mantata ba, dan haka ya tura mata voice din baki dayansu, a lokacin har an fara kiraye kirayen sallar magariba, ama babu wanda ya yi alamun zai tashi dan gabatar da abinda zai kwace su gobe kiyama, sai suka fi gane karasa zancen da suke gannin shi ne a gabansu a yanzu Da yannayin mamakin jin abinda ya sake fada mata na Wacece RAUDA kamar yadda Nafeesa ta sanar masa a lokacin da ake rade radin an yi mata shashawa ya je ganewa idannuwansa tsaf ya zube mata, ya dora da fadin" Ni baban abinda ya dameni shine ganninta a jikin Hajiar sarakai, to me hakan yake nufi?" Da wani bacin ran da kuma mamakin karfin halin Rauda Amnah ta danna masa kira, yana dagawa ta ce" Kana ji? ka tambayi kawar nan taka ta sanar maka dalilin da ya hadata da dangin mijina, ina jiranka komai dare ka ji?" Sosai ya gane akoy baban abinda zai hada Amnah da RAUDA, dan Amnah bata cika bin didigin abu ba, idan ka shiga hanyarta ka kure bata mata rai a sawake zata saka a koya maka hankali ne, dan ta zuba makudan kudi a daukeka a baka wahala baya ce mata komai, dan haka da gagawa ya dannawa Nafeesa kira, ya ringa yi mata tambayoyin har ta dire masa aya, ayar da ta firgitashi, dan tunda akace Balarabe mai kyautar manya ya rasu, kuma dukiyarsa ya barawa matar da ya aura gaba daya dukiyarsa yake cigiya da neman Wacece, dan kuwa burinsa ya ji ko Wacece ta yadda zai je ya zama ɗan dakinta, dan ya san idan ya samu karɓuwa ya warke daga cutar talaucin dake damunsa, sai dai wata cutar ba dai wannan ba Bayan ya kashe kiran ya jima yana tunanin amsar da ya dace ya sanarwa AMNAH, dan kuwa ya fi so ya fara jin musababin neman Sannin Wacece RAUDA da Amnah ke yi kafin ya san irin amsar da zai bata, saboda nasa aljihun ba dan komai ba! A lokacin da ya yi kiranta sanar mata ya yi gashi ga Nafeesa ama tace sai an dire mata kudade zata fadi wacece RAUDA Amnah kuwa a lokacin an zo yi mata kwaliyar be kamar yadda ta buƙata, a dole ta sasauta maganarta kamar yadda mahaifiyarta ta fada mata, cewa ta kula daga nan har a sadata da dakinta ta kiyaye duk wani abin da zai sa ta shiga ido ko bakin makiya, ta bari har ta je ta ga takun uban kowa kafin ta maida martani daidai da amsar kowa A hankali ta furta" Ka ajiye min accunt numba, ama ka tabatar har tarihin uban ubanta ka jiyo min da kuma abinda ya hadata da dangin mijina ka ajiye min labarin a nan zan saurara idan halin saurarar ya kama!" Jiki na bari ya tura mata account numbar, sannan ya fice a restaurant din ko sallar bai yi tunanin yi ba yace sai ya gama kashe wannan wutar zai yi, ya haye mashin dinsa ya nufi gidan su Nafeesa, dan samun cikakken bayani daga bakinta ya sanarwa AMNAH, dan ya san yau sai ya shaki kudin da bai taba shaka ba a zamantakewarsa da ita, tabas ya san akoy balaki kuma in sha Allah sai ya karu da wannan balakin! Tana yin transfer na makudan kudi ta maido hankalinta kan mai kwaliyar da aka kawo mata kwarai ta san masu kwaliyar, sun iya kwaliya sosai domin yarinyar a wajen Hajia NAJEEBA ta koyi kwaliya ta bude saloon a nan garin, sai dai ta so ace HAJIA NAJEEBAR ce da kanta ta zo yi mata kwaliyar, dan ta nuna mata a yanzu fa ba maganar da ta taba fada mata wani lokacin da dan karamin abu ya hado su, ta ce a sanar mata ba zata iya taba fuskarta dan kwaliyewa ba, kuma tace a sanar mata eh lalle kwaliya sana'arta ce, ama fa bata cika yiwa wa'inda suka tsinci kudi daga sama kwaliya ba, dan basu iya barnar kudi ba, sunna zubawa sunna tuna sabulun da zasu saka su wanke hodar ne, wanda ke cikin hajar kuwa ya shafa hoda yanzu ya wanke baya ce masa komai, sosai maganar nan ta mata zafi dan a lokacin kawai cewa ne ta yi a ce mata ko nawa ne kudin kwaliyarta ta fada mata ama so take ta zo ta yi mata har Tsatsunburum , a lokacin batama auri SHAHEED ba take iya yin nan, ta so ace itace aka turo mata yau, dan ta maida mata magana walahi, sai dai ba laifi, zata sanarwa wannan dinma dan ta tabata sako zai je inda take so ya je! Bayan ta zauna ta cire hular dake kanta mai dauke da katon ribom din da ta makalawa gashinta tana kallon mai kwaliyar da yaranta biyu masu kama mata aikinta dan ta zo da su ne saboda Salima tace harda gyaran kai zasu yiwa Gimbiyar , dan su gama mata da wuri, cike da isa bayan ta wani watsar da su din nan ta ce" Azl 47 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo DA isa ta ce" Kina da abinda zaki saka min a kai ne? ko in sa a kawo? koda yake na so ace uwar gidanki ce ta zo dan ban sani ba ko ke kin iya abinda ta iya?" Kallonta mai gyaran ta yi tana sake maimaita "UWAR gidana?" Amnah ta dan dage kafadu ta ce" Eh NAJEEBA" Ido ta dan zarro tana dubanta, sai kuma ta yi murmushi kawai bata ce mata komai ba, dan kuwa wannan amsar ba zata bata ba walahi, san ta sani NAJEEBA ba sa'ar yinta bace, , a ranta kawai ta ayana' Ikon Allah, dama haka kan Amnah din nan yake? to wai isar nan da take yi na menene? koda yake haka akace halinta, dama ance yan gidansu sun ce sun fi karfin saloon dina ko me?, sai dai ki yi hakuri Ni ba zuwa na yi ki bani sadaka ba, kuma a yadda na yi aiki karkashin Hajia karya ne dan zan maka aiki ka raina Ni, ta koya mana Sannin ciwon kanmu, Hajiarmu kuwa daidai take da ke ki yi haukanki ya kai kunnan ta!!' A bayane mai saloon tace" Muna da atach natural, in kuwa basu miki ba sai a sa a kawo " Amnah ta dan dubeta, gannin ta bata amsa kai tsayen nan, ama bata ce komai ba ta sa suka bude atach din nasu kwarai manya ne masu kudi ne sosai, dan haka kawai sai ta zabi wata mai kama da gashinta sak, kuma mai tsayin gaske ce ta basu dama suka shiga kimtsata A cen wajen Habu dan daudu kuwa yana zuwa wajen Nafeesa har gidansu ya shiga, a falonsu ya zauna suka fara zancen, gannin tana zazagayewa ya bata jaka na bin jaka har ashirin , kyautar da ta bata mamaki, dan da wahala ka ga ko jaka guda ce dan daudu ya cire ya baka, sai dai bata tsaya masa kwana kwana na, da banzarta ai zata sanar masa dukkan abinda yake son ji hankali kwonce ne Dukkan wani bayani da yake son ji sai da ta sanar masa, bata sani ba recoding dinta yake yi daya bayan daya, tun daga kan accident din iyayen RAUDA, rikon da uncle dinta ke yi mata da matarsa, sanadiyar komawarta hannun Mah, da aurenta da Balarabe da mutuwar auren ta karashe maganar tana fadin" Kamar yadda ka sani ko ka ji ana fadinta a gari hakane, mutun ce mai shegen son kudi , bata soyaya da kannanu, kai ko hulda bata yi da talaka ka yarda da ni, na yi mamaki ainun da na ji inda ta koma rayuwa, sai Ishak ke sanar min mahaifiyar sir ce ta dauketa sanadiyar accident din da suka yi shi da ita a adaidaita, duba ka ga Sa'a irin ta yarinyar nan fa? kuma lokaci guda ABDALLAH din nan ya aureta, kuma wata muguwar sa'ar mijin ya mutu ya bar mata komai? kai mu dai mu muka wahala ba soyayar ba ba neman kudin ba!" Yana sakarwa Amnah labarin ya sake bararajewa bayan ya sauke data ya ringa jin sauran firarakin dake iya gyara shi, misali mu'amalarta da mutane da sauransu, yana ji a jikinsa shiga FADAR TSATSUNBURUM ta kama shi koda a matsayin dan aiki ne dan shima ya samu nasa rabon, kuma ya karra yarda akoy wani abin da ya hadata da Amnah, wanda yake son sani , kuma ya san AMNAH zata fada masa ne da kanta, zai dai je ya daki cikinta cikin hikima har ta zayane masa komai ba tare da ya sha wahala ba, 'Hum, ina tsoron wannan karron uwar dakina ta janyo abinda yake iya rinjayar hannayanta ko ya makata da kas, domin idan dai takamar ta kudi ce bana tunanin mai yinta da na wani da mai yinta da nasa su zo daya, dan kuwa malan bahaushe yace da namu gwonda nawa, ba za'a taba hada mai yi da na iyayenta da mai yi da nata ba gaskiya!' Shine abinda ya yi ta ayanawa a ransa ..................................................... Abincin take zubawa a plate plate da miyar zabin da ta yi, Har yanzu jikar girarta bata bushe ba, dan tana gama daidaita miyar ta shige dakinta ta yi wanka ta cenza tufafi zuwa sket da riga na atampa ta saka hijabi ta yi sallah sannan ta cire ta yafo mayafi dan madaidaici ta dawo falon dan idasa aikinta, domin tunda suka dawo Salima ta sanar mata Mah tace a karra yawan miya saboda bakin da zasu raka Amnah dakinta A hankali take aikin , Salima kuwa na dauka tana kaiwa bakin dake cen karamin falo da kuma daki wajen yan kwaliya, wa'inda ke aikinsu ka'in da na'in Tana gama zuzubawa ta juyo dan duba agogo saboda maganin Mah da kuma lipton dinta na dare da take sha, sai ta ga Mah din tsaye a kofar shigowa ta harde hannayenta tana kallonta Murmushi ta kakaro tana dan buda idannuwanta ta ce" Lah, Mah tun yaushe kike tsaye a nan? ban fa ganki ba" Mah ta idasa shigowa tana murmushi, a ƙalla ta kai minti biyar a tsaye a wajen nan, ama RAUDA bata san ta zo wajen ba, ta afka tunani ne ko aiki ne ya mata yawa?, dan haka da kula ta ce" Na jima a tsaye fa baby, ki je ki huta aiki yau ya maki yawa, je ki yi sallar isha'i ki huta kin ji?" Murmushi ta yi ta karasa ta dauki abin dafa lipton din Mah, ta je ta bude wajen kayan shayin ta harhada dukkan abubuwan bukata, dan shayin ba wai Mah din kadai bace ke sha, harda MALEEK, tana juyowa Mah ta ce" Lah rage kayan nan, yau ki dafa iya nawa, shi da za'a mika masa matarsa yau ai zata dafa masa abinsa ya sha ko? ko aure zan masa in ci gaba da bashi tuwo?" Mah ta karashe zancen tana sakin murmushi, RAUDA kuwa sai ta tsaya cak tana kallon Mah din har sai da Allah ya sa ta tuna tsayuwa ne ta yi sannan ta juya da sauri tana lumshe idannuwanta ta koma wajen abin shayin ta bude ta ringa rage kayan, inda Mah ta bita da kallo tana kausasa idannuwanta kafin ta girgiza kanta ta juya ta fice a ranta tana ayana' Lalle zaku san kun yi da mamanku, daga ke har shi mararsa wayo kawai!' RAUDA kuwa kayan shayin ta rage ta koma wajen abin ruwan nan ta wanke su tas ta zuba ruwa ta dora sannan ta ja ta tsaya a hankali ta rungume hannunta a kirjinta, tana jin ranta na tafarfasa sam bata san har ya dahu ba, sai da kukan butar ta sakata juyawa da sauri ta mika hannu ta kashe gaz din sannan ta dauko abin juyewa ta juye komai ta juya da su ta fito a nutse ta nufi dakin Mah ta kai mata shayin da kuma maganinta Maganin ta tsaya sai da Mah ya sha sannan ta ajiye sauran ta nufi dakinta ta shige ta rufe da ky Tana rufewa ta ja ta tsaya kanta na sarawa , idannuwanta na yi mata nauyi, kirjinta kuwa na yi mata zafi A hankali ta karasa wajen madubin dakin ta ja ta tsaya ta tsurawa fuskarta ido dan kwalin kanta ta cire a hankali ta ajiye gaban madubin sannan ta saka hannu ta cire ribom din kanta dan siriri fari shima ta ajiye kafin ta zubawa fuskar tata ido Hawayen da idannuwanta suka tara take bi da kallo, zuciyarta ba tsintsinkewa da wani fitinanen tashin hankali Ta sha tsayuwa ta dubu kanta tace da kanta RAUDA kin ji kunya, RAUDA kin saka kanki a uku tunda kika ce wannan rayuwar zaki yi, me kike nufi RAUDA? Yaushe mijinki ya rasu, abin kaunarki, wanda ya nuna maki so da gata tunda ransa sannan ya rasu ya kuma Bara maki wani lasisin so da gatan a duniya wanda koda yau kika rasa mai kama hannayenki da izinin Allah ba zaki tagayara ba in dai kin kiyaye dokokin Allah, sai dai kashh, tun kafin a shafe shekara ke RAUDA shine kike tunanin wani abin da ba zai taba fisheki ba?, me aka yi aka yi namijin da ya cika takama da jiji da kai? RAUDA babu so a wajen da ba za'a iya fadarshi ba, ke mace ce mai daraja, furta so ba rashin daraja bane, ko alamuntawa, sai dai ke taki darajar abar dubawa ce RAUDA!, kin jurewa lokacin da baki da mai maki fadama bale yanzu? me aka yi aka yi soyayar kanta? RAUDA ki kama kanki, kar ki yi abin Allah wadai, RAUDA ki kama kanki!' A hankali ta lumshe idannuwanta daga kallon fuskarta, a nutse ta janyo kujerar gaban madubin ta zauna ta sake dago fuskarta ta tsurawa kanta ido A nutse ta shiga yiwa kanta kalaman da zasu fisheta, wa'inda ta tabata in dai ta rike to kuwa tsaf zata tsira da mutuncinta, a tausashe ta shiga ayanawa kanta magana kamar haka' Ke mutun ce kamar kowa RAUDA, kuma Allah na iya jarabtarki da abinda ke iya yi ke iya rikitaki a rayuwa har ya zo ya nemi zame maki AZAL, sai dai idan har kin rike addu'a babu abinda zai same ki, mummunar kadararki zata juya ta dawo kyakkyawa......., RAUDA kin kasance mutun mai tsare tsare da addu'ar kalar mijin da kike so a rayuwa, misali bakya son namiji mai shegen son mata ko aure aure dai da sauransu, to a kan me zaki dubi mutumen da kafin darajar sarauta ta hau wuyansa ya kasance mai rike da darajar sarautar bakin layi wace kowace yan mata ke wawarsa?, Haba RAUDA a yanzu da igiyar daraja irin ta sarauta ta hau kansa ke da kanki kin sani karya ne ace dayar nan ce, bayan wannan ki duba ki gani, ke da aka raba ake girmamawa aka ba daraja yau ke ce da zagin matarsa?, idan Mah ta ji ki ce me? hana RAUDA me ya kaiki wannan gangancin? me yasa ba zaki ci gaba da tafiyar da rayuwarki yadda take ba?, Eh lalle YUSUF shine AZAL din ki!, sai dai kuma addu'a da neman tsari ai yana maganin komai ko RAUDA?, kema mutun ce mai rai da lafiya kina iya gannin mutun ki ji ya maki, ama kuma kamar yadda kike iya gani ki ji ya maki kina iya kawar da kanki a kansa, bale idan mutumen nan kin gane take takensa, shikenan ke da shi sai ki yi ta neman tsari, ke wai menene soyayar kanta? ake rayuwa ba soyaya kuwa lafiya, to kema daga yau ba ke ba wannan maganar, bale ke da Allah ya taimaka ganninsa sai idan kin so? baki ganshi Bama bale har hankalinki ya nemi gushewa RAUDA!' Magana take yiwa kanta idannuwanta a lumshe a cikin zuciyarta, kuma har ga Allah maganar ta Ratsa ilahirin jikinta ta yarda da hakan, domin a yannayin nan da take ciki kunnayenta suka ringa jiyo mata Muryar Jakadiya baba tana bada umarnin a kama alkyabar uwar gidansu, a yi me a yi me A hankali ta dago idannuwansa sakamakon shigowar da Salima ta yi tana kiran sunnanta Ido hudu suka yi ita da Salimar Salima na dubanta ta ce" Dear, me yake damunki ne? yau ko baki da lafiya ne babyn Mah? taso mu raka aunty Amnah mana Gatacen sun fito Su Bah na yi mata nasiha" Murmushi RAUDA ta kirkiro a hankali ta dan rausayar da kanta tana kallon Salima ta ce" Sisi am, zan yi sallah ne na dan yi karatu, ki je zan tardo ku idan baku dawo da wuri ba in sha Allah " Gyada kai Salima ta yi ta yi mata murmushin itama sannan ta juya ta ja mata kofar a nutse Mikewa RAUDA ta yi ta je ta rufe kofar da ky sannan ta nufi bayi tana sake dannar kanta , fadawa kanta take babu wani abinda ke damunta da su baki daya, sake fadawa kanta take yi ko me zata gani ko ta ji ba damuwarta bace in dai abinda ya shafe shi ne da matarsa, kuma in sha Allah daga shi har matarsa ta yiwa kanta alkawarin zata fita a harkar su , ba ita ba su bale ranta ya ɓaci! Tana gama wankan da zata je barci ta saka tufafinta doguwar riga a saman pant dinta kadai ta daure gashinta sannan ta shiga gabatar da sallar isha'i, tana gamawa ta dora nafilar sannan ta cire ta shafa turarukanta ta je saman gadonta ta sake kakabewa ta yi kwonciyarta tana dora wayarta saman abin gadon bayan ta kashe fitilar dakin Da addu'a da juye juye da kyar ta samu barci ya fara fizgarta, hakan ya sa bata san ta dauki lokaci a kwoncen ba, kamar wace ta je duniyar da bata san abinda take yi ba ta dawo haka ta tsinci kanta, har sai da ta ringa jin amon kiran wayarta sama sama sannan ta bude idannuwanta tana jin gabanta na faduwa ta lalubo wayar da sauri ta duba screen din ta ga sunnan Mah ke yawo a sama da sauri ta daga muryarta na shakewa ta furta"Mah?" Mah dake zaune a falo ita da YUSUF takaici ya isheta, sai shayinsa, ta shiga ta dafa masa wai ba shine ta saba bashi ba, ta tambaye shi wani irin dandano yake so yace shi bai sani ba shi dai wanda ta saba bashi idan ya zo, ita kuma tunda RAUDA ke hada mata tea bata taɓa Sannin me da me take haɗawa ba, ita dai ta san da ta mata wani mai dadi tace ta ringa yi mata shi kulun bale da ta sanar mata tana haɗawa harda kafi amarya kanshi saboda yana karra lafiya sai kawai tace a rike hadin da Kula da kuma yannayin tausayinta Mah ta ce" Daughter, kin yi barci ne? idan kin yi barci yi kwonciyarki kawai" Dirowa ta yi daga saman bed din har tana yarda hularta saboda murya Mah sai ta ji kamar bata da lafiya ne, ko abin barci ne ya sa ta ji haka? ita dai da sauri ta ajiye wayar tana fadin" Gani nan zuwa" Bata tsaya daukan hijab ko wani abin ba, tsoronta daya kar aje jikin Mah ne, dan lokaci zuwa lokaci ciwonta na tashi, shi yasa ko yanzu ta fice daga ita sai doguwar rigar nan da ta sauka har kasa, sai dai tana da tsaga daya jal daga gefen cinya, gashin kanta daga gaba ya kwonta lambuk daga baya kuwa du ya nanade irin na masu gashin nan, dama dama tana da dan dogon hannu kadan rigar, ama bayan wannan rigar mai lafewa a jiki ce sosai shi yasa harta sawun pant dinta ana gani Da sauri ta bude dakinta, kafarta sanye da takalmin daki na kusa da gado mai gashin mage mai kalar pink ta nufi dakin Mah da sauri Har zata kama ta bude kofar, Mah ta furta" BABY?" Da dan sauri ta juyo inda ta ji Muryar na Mah, sannan ta juyo da dan sauri kadan ta karaso ta kai zaune daf da Mah tana fadin" Mah jikin ne? ina ke ciwo? kafar ce?" Mah ta sauke murmushi tana jin kaunar RAUDA har cikin zuciyarta ta kama hannayenta ta ce" Baby Lafiyana kalau, sorry daughterna na tasheki ne ko,?" Sai kuma ta juya wajen da yake hakimce cikin shigar kayan barcin shima masu duhu da santsi tana kallonsa ta ga lokacin da RAUDA ta sauke ajiyar zuciya jin lafiyar mah kalau ta ce" Ji fa rikicewa, shi yasa nace ta yiwu ta yi barci, tashi ki je ki yi kwonciyarki, ko ki nuna min yadda ake yi na nuna masa ya je ya koyawa matarsa ta dafa masa, barima ka ji mun cire ka a kwanon abincin part dinmu tunda mun maka aure!" Tamkar an dakatar da ita haka ta ja ta tsaya a zaunen nan gabanta na wani irin mummunar faduwa Da kyar ta iya daidaita kanta bisa kwarin gwuiwar da ta ba kanta ta dan saki murmushi ta mike tana dan susar kai ta ce" A'a Mah bari in je in dafa" NA SAKA BONANZA TA NOVELS DINA BAKI DAYA A KAN FARASHI MAI RAHUSA 1K IN SHA ALLAH, KI TUNTUBENI BISA NUMBANA LAMAR HAKA 93811618 Azl 48 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo Mah ta bi yadda du ta dan daburce kadan, a yanzu ta gane a yadda ta fito bata san da wani bayan ita a falon ba, tana kallonta ta nufi dakinta da sauri tana jan rigarta har ta shige, minti kadan ta fito sanye da zumbulelen hijab dinta wannan karron yannayinta ya nuna ta samu nutsuwar tafiyar ko dan ta suturce jikinta ne ko meye? a nutse dai ta nufi kicin din ta bude madubin ta shiga ta rufe Murmushi Mah ta yi a nutse ta juyo dan yi masa magana, sai ta ga idannuwansa a kan kicin din duda bata nan , dan ta jima da rufewa, kuma yannayin fuskarsa ya dan kame kadan da yadda suke shan rikici tun dazu a kan tea dan da ya taba wanda ta dafa fuska ya tubure shi dai ba wannan ba kuma ya saba idan bai sha ba kansa ciwo yake yi masa, da tace Baby ke dafawa kafada ya daga irin shi dai ba ruwansa ko waye shi dai tea dinsa ya sani Mah ta dan yi murmushi ta dan motsa dan tana so ya ji abinda wata fada Cikin dabara ya dauke dubansa ya dan murza hancinsa sannan ya dubi Mah a nutse ya furta" Na gaji sosai yau Mah" Mah ta yi murmushi tana fadin" Sannu d'an Mah, kana gani yarinyata ma ta gaji ka sa na tasota, yarinyar nan Allah Ubangiji ya nuna min ta samu miji na gari ta yi aurenta itama ta haifi wa'inda zasu bauta mata da jikinsu da lafiyarsu kamar yadda take hidima da Ni" Dif ya yi, maganar da Mah ta yi ta saka shi yin shiru na yan dakiku kafin ya dago dubansa ya kalli Mah sau daya sannan ya dauke duban nasa yana dan dantse lebensa, a ransa yana ayana' Uhum, yanzunma ai ta haifa sai ya mata hidimar, Ni banma san takabar nan ta meye take yi ba, ko kafin ya rasun sai da ya mata wani abu shi marar jin tsoron Allah?, koda yake ba wace bata jin tsoron Allah sama da yarinyar cen, tana kallon mutun ido cikin ido ta iya raina masa wayo da yin tamkar bata san me yake yi ba, har Ni zan hanneta abu ta aikata, kuma ta ci gaba da kallona ido cikin ido, gata in kasheta ko? ba abinda zan maki RAUDAhhhhhh, ama bana jin in zan iya yafe maki, ba aure aure ba? bismillah ki sake yin wanin sai me daga ke har maman naki!' "Magana nake yi YUSUF" Mah ta fada da dan karfi tana dan daga hannunta, dan sau uku kennan tana magana bai ce mata komai ba kallonta ya yi da dan sauri yana furta" Na'am?" Mah ta fara magana RAUDA ta fito dauke da wata mahaukaciyar butar shayi da kofi na kwalba a saman plate dinta , a lokacin ne Mah tace" Yaya ina ta addu'a har sau uku ba zaka ce min amen ba? na yi maganar Allah ya ba y'ata miji na gari , baka ce min Ameen ba, na yi maganar Allah ya baku zaman lafiya ya kade duk wata fitina baka ce min amen ba, na yi maganar taimako da aka bayar wa mazan masu mana hidima Allah ya karra budi shima baka ce min ba fa" A hankali RAUDA ta ajiye plate din a saman dan madaidaicin teburin dake dauke da taya biyu kadai wa'inda ake kafe su idan ba'a so teburin ya motsa, kuma ana sakin su idan ana son motsa shi, a nutse ta sake su sannan ta turo teburin har gabansa ta kafe masa shi, a nutse ta dauki dan karamin kofin ta zuba tea din sannan ta dauki zuma ta bude ta tsiyaya madaidaiciya ta saka dan karamin cokali tana motsawa a hankali ta dago idannuwanta jin ya yiwa Mamanta shiru bayan ana masa fada ko dai ya tafi ne?, sai ta ga yar yatsarsa ya kai wajen sajensa a hankali yana dan shafawa lebensa na fitar da alamun murmushin fadan da Mah ta dage tana yi dan kawai bai ce wai amen ba Mah ta turo baki tana dauke kai, shi kuwa a hankali ya furta" Amen Mah" Sai kuma ya juyo dan tunda ta fito ya ga fitowarta har zuwa yanzu Hannunsa fari sal ya miko ya amshi tea din, idannuwansa a kanta da kallon da ya sake sakawa zuciyarta idasa hautsinewa kafin ya dauke dubansa yana sauke ajiyar zuciya a hankali ya kai kofin bakinsa Da dan sauri ta furta" Bai huce ba fa!" Mah da ta yi kamar bata nan da gangan dan zata so ta idasa ganewa idannuwanta ta sake dauke kai dan sai ta ji kunya na son kamata bayan ba wani abin suka ce ko suka aikata da zai iya bata kunyar ba, haka kawai dai ta ji inama ace rana ne sai ta bugawa wani kira ta bar wajen ko sa gama rainawa junna hankalin Idannuwansa ya sake sakawa a cikin nata, da kaifin da sukai masa shi kansa zuwa ita da ta ji kamar zata lume ciki, yana kallonta yana danne harshensa da hanna kansa yi mata tambayar nan daya jal, cewa wai takabar me kike yi? ke takabar me kike yi? dan Allah takabar me kike yi? ama ya kasa dan ba zai so a masa wata fasarar ba, ga Mamanta nan zaune, sai kawai ya yi mata horon da ya fi sakata yin laushi ta hanyar amfani da idannuwansa ya ci gaba da surbar tea din da ta bashi bayan da zafin sosai Ajiyar zuciya ta sauke a hankali ta dauke idannuwanta a kansa ta juya ta karasa wajen Mah a tausashe ta furta " Good night Mah" Mah ta dubi fuskarta, du ta yi yaushi kana ganninta zaka ga cenzawar yannayinta, ta yi mata murmushin itama tana fadin" Good night baby, Allah ya miki albarka, ama daga yau ba za'a kuma taso ki saboda tea ba, zaki koyawa matarsa ne!" A ranta ta ayana' Allah sai dai kar ya sha!' Shi din kuwa ya ayana' Ita din dai zata dafa shi, wa ya sa ta saba min!' A raunane RAUDA ta kai zaune tana sake jin irin yadda kirjinta ke yi mata zafi da ɗaukan mugun abinda ta gama yi masa fada dazu, sai dai kasancewar addu'a ce baban makamin da ta gama yarda zai zamo makamin yakin duk wani abinda ke kawowa zaman lafiyarta farmaki sai ta ringa jin sassauci da salama a cikin zuciyarta da kuma dangana, karshema sai ta dauko yabon mamaci ta yaba a zuciya ta bige da yi masa addu'a kamar yadda ta saba har barci ya kwasheta tana yi masa addu'a bata sani ba. Ya dan jima tare da Mah, har sai da ta kore shi sannan ya mike ya nufi hanyar da ya biyo ya fice ya nufi bangarensa Ya bude ya shiga mamakeken falon da ya raba bangare bangaren ginnin har sau biyar Kwarai ya san dama a nan ne za'a fara ajiyeta matsayin bakuwar wajen, kuma ya tabata da wahala ya tardora a rufe kamar yadda bakin amare ke yi, dan tuni ya gama gane wannan fa idan ba'a gama raba hajar a titi Bama da sauki sauki dan yannayinta yannayin tafiyar kayanta Tun da ya shigo AMNAH ta ajiye wayarta, waya suke yi da mahaifiyarta duk irin tsayin daren nan da kuma kasancewarta amarya tana sanar mata dukkan abinda aka yi daya bayan daya ita kuma tana shawartarta abinda zai fishe su Murmushi ta sake yi masa tana dan sada dubanta, dan duk yadda take son kallonsa ido cikin ido sai ta ji ta gaza jurewa, bata san yaya aka yi shi baya jin nauyin kallo ko kadan kansa ya dan kawar yana sauke ajiyar zuciya, da kyar ya danni kansa ya karasa saman falon ya zauna yana sake dubanta da tunanin abinda zai yanke a yanzu Dubansa ta yi da wata murya ta kisa ta furta" Barka da shigowa ur majesty" Idannuwansa ya dan lumshe a hankali, hakan ya tabatar mata amsar kennan, sai hakan ya sake saka mata dan shaku da gudun cika surutu ya jima a hakan, yannayinsa a mace gaba daya sannan ya mike a nutse da nufin tafiya nasa bangaren Mikewa ta yi zungwai zungwai ta bi bayansa har sai da ya dan dakata ya juyo a nutse yana dubanta Ba da niyar wulakantarwa ba, dan ya riga ya amsa ko mecece, kamar yadda ya gama yarda cewar ya rungumeta shine zai sa ya manta abinda ya fi komai tsaye masa a rai, ya dubeta da kula sosai , da irin izar mulkin da yakan yiwa na waje wa'inda ba Mah da Bah da kuma Hajia ba ya furta" na san kin gaji yau ko?" Dubansa ta yi da sauri, dan irin yadda ya yi maganar yana dubanta sai da gabanta ya fadi Dan murmushin da ya sakata shakun anya murmushin ne? ko ba murmushin ba ya yi mata a hankali ya furta" Ki je ki huta, ga part dinki cen........sweet dream....." Ya karashe yana juyawa ya karasa nasa part din ya bude ya shige sannan ya rufo kofar a hankali ya karasa wajen bed dinsa ya shiga kashe fitilun dakin ya kwonta yana janyo carbinsa a hankali ya rintse idannuwansa hadi da rukunkume fillon dake saman gadon yana jin yadda zuciyarsa ke mugun bugawa...... Bai taba zaton za'a bashi harka a bude ya kasa karba ba, bale harkar nan ta halal, matar aurensa, duk irin yadda ya rike kansa tsayin lokacin nan shi kadai ya san cikin azabar da yake shiga wasu lokutan idan yana cikin happy, na bukatar mai ɗebe kewa, gata ta samu ama wani lamari mai ban haushi ya hanna shi rawar gaban hantsi?.....in sha Allah zai ture, zai ture dan ya fuskanci matarsa su yi irin zaman da ya dace da su, na mutunci ko na abokin gabar mutunci dan duk abinda ta zo da shi da shi zasu kafta..... AMNAH Kam......., sai ta ji wannan abin da ya yi wata dungumemiyar nasara ce, dukda ta so ace ta kwana a dakin, sai ta bar hakan zuwa ta hutan da yace ta juya tana jin farin ciki ta nufi dakinta ta sake kunna wayar dan tana son sauraron voice din Habu dan daudu, sai dai tsarin dakin nata ya sakata sake shagala kamar yadda ta shagala a falon nan ta ringa yiwa mahaifiyarta vidion falon haka yanzunma ta ringa yiwa dakin vidio tana turawa a wayar mahaifiyarta sannan ta danna mata voice note tana sanar mata tabas kayan nan sun ninninka nata da aka kawo, ita batama ga natan ba, kai kayan nan sun haukata ta fiye da tunani dan ta jima tana sake dauka har bayi sannan ta zauna sai kace ba itace ke takamar daga gidan kudi ta fito ba, zuciyarta ta sake cika da wulakanci da tarin dagin kai, a yanzu ta gama yarda tana iya bin Mah ko dan ta sayi zuciyar d'anta, idan yaso daga baya ta yi mata zagon kasa dan ta gama ganewa idan har ta idasa baban haja komai ya kare, a yanzu ba wai iya kasar nan ba o ko waje ta fita daidai take da uban kowa! Da wannan ta zauna bakin gadonta ta shiga sauraron Voice din Habu tana cire uban lulubin da aka yi mata da rigar da aka saka mata a karkashin lulubin Tana sauraro ne bakinta da idannuwanta na buduwa zuciyarta na tafarfasa wani irin takaici ya gama lulubeta a lokacin da ta kusa gama sauraron maganar da takaici ta datse , sam bata ji bayanin aurenta da Balarabe da dukiyar da ta samu ba, a bayane ta furta" Da ke karamar fakirar talaka ce har kika budi baki kika zageni dan uwar mijina na rikon ki?" Idannuwanta ta lumshe cike da ture tunanin dalilin dake raya mata yana iya sakawa RAUDA ta yi mata haka a bayane ta sake furta" na san ko giyar wake kike sha ke ba zaki so mun miji ba, kuma na san ko tube ki aka yi a gaban mijina a halayan da aka fada min nasa na da ba zaki dada shi da kasa ba bale har ya tanka, domin wanda yake amini a jikinsa ya sanar min irin matan da ya yi mu'amala da su ba kannanun kadangarun bariki bane!, walahi Ni na san tunda na ga matar nan matsayin mamansa sai ta ja min matsala, ba damuwa na sayi fadan ki Ni da ke za'a ga karamin dan iska, in dai ina raye walahi sai na ga bayanki kafin na ji ubanda ya tsaya maki har kike zagina, tunda na ganki na ji na tsane ki, ashe dan talaka ce ke? mtssssss!" Sosai ranta ya ɓaci, hakan ya sa ta ci alwashi sosai a kan RAUDA, kafin ta yi kwonciyarta dan ko fitsari bata ji, kuma ba zata wanke kwaliyarta ba dan tana so gobe da safe ma ta birgeshi da ita, shi yasa ta gama kudurcewa ranta salolin zata hade kawai zuwa gobe ta gani ........ ( Uhum!) Washe gari haka aka yi yar hidimar girki aka kai bangaren, ama Mah ta hanna RAUDA taɓa girkin dan tunda ta tashi da asuba ta ji jikinta da zafi, shi yasa ta sa ta je bangarenta ta kwonta, har dare a bangaren nata take sai da aka yi sallar isha'i ta sa ta je ta kwonta domin da sauki kawai dai rashin kuzari ne, Mah ta alakanta hakan da matsowar cikawar tabakarta jibi jibin nan, shi yasa take ta yi mata nasiha da rarashi har ta samu ta kwonta a kwana na biyu kuwa su Atu suka dauke mata hankali, dan sun sakata gaba wai sai an yi mata kitso da kunshi na fita takaba ita kuwa tace ba zata yi ba gaskiya, sunna shan fira sunna ɗebe mata kewa har Mah ta shigo ta sanar masu zata je bangaren Hajia ta yi kiranta tace ta je SULTAN SHAHEED na son ganninsu har ya karaso, suka yi mata a dawo lafiya suka ci gaba da firarsu a tsakaninsu, Firar da rabinta kokarin nunawa RAUDA ne cewar hakuri zata yi na rashin mijinta, addu'a itace abinda zata ci gaba da yi masa har ta koma ga ubqngijinta na nuna Soyaya, ama a yanzu kuma da ta fita a takaba shikenan , duk wani abinda ya dace yi za'a yi, walahi ko bata yi kitso da kunshi yau ba sai ta yi gobe....... Ita dai walahi zazzabin dake mata ya je ya dawo ya fi takurata, dan ta kiyewa Mah maganar asibiti ne, gani take yi daga dan zazabi sai asibiti? ama nukurkusarta yake daidai misali! Da girmamawa, da kula ya fara gaishe da su, a kujerar da yake zaune wace take facing din su Hajia baba bata san da zuwansa ba, sai da aka shigo aka sanar da ita, kuma yau YUSUF ya yi yar tafia tunda asubahi ko da ta kire shi, shima jim ya yi yana tunani yace yana zuwa, da ya kira shi sai yace da shi zuwa ya yi kawai gaishe da Hajiar, hakan ya sa ya sanar mata da gagawa aka shiga tarban SULTAN SHAHEED. Mah na murmushi take sake tambayarsa takwarar Anmi Sarkin rigima, yana murmushin shima ya ce" Tana lafiya Mah, ai kam zata zo maki hutu ko na dan huta da rabiyar fada ita da yan uwanta" Hajia na daria ta ce" Allah ya nuna mana, da mun yi farin cikin hakan" Ya amsa da amen, sannan ya yi shiru na dan lokaci, kafin ya dago kansa da girmamawa da kalamai irin wanda zaka yiwa baba magana da su ya ce" (😨😨😨😨😨😨😨) Azl 49 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo A nutse, cike da girmamawa bayan ya dago ya dube su , sannan a tausashe ya ce" Ina mai baku hakurin zuwan ba zata da na yi, na tabata idan har ya san zuwan nawa yana gari zai iya biyoni ne, idan kuwa yana zaune firar ba zata yiwu ba, bayan abinda yake tafe da Ni mai mahinmanci ne" Hajia ta dubi Mah, Mah kuwa ta sake tsura masa ido tana addu'ar Allah ya sa ba wani abin ne ya samu YUSUF din ba, dan sukan yiwa junna haka, a baya idan YUSUF ya bata mata rai ta ki hakura shi yake zuwa ya wani kalamaiceta, shi yasa a yanzunma tana kallonsa tamkar zata ciro maganar daga bakinsa take ji A tausashe ya dan nisa ya ce" Dangane da maganar RAUDA ne" Mah ta dan zarro ido, Hajia kuwa ta dan matso gaban kujerar tana dafe kirji tana kallonsa, sai kuma ta shiga salalami tana fadin" Yi bayani mana Sultan, me ya samu baiwar Allah marainiyar Allah?, me ya sameta?" Hannunsa ya dan kai wajen hancinsa kadan dan maganar da nauyi a yita da iyaye, kawai ya ga ne abokinsa akoy taurin kai shi yasa ya zo din kai ya sake maidawa ya sada a tausashe ya ce " Tun kafin aurenta da ABDALLAH, MALEEK ke son ta", Ya ajiye maganar a hankali yana dan dago idannuwansa ya sauke dubansa a fuskar Hajia da ta saki baki ta zarro idannuwa ta kuma dago hannu kamar zata tare wani abin, sai ya ga Mah kuwa babu irin matsanancin mamakin nan a fuskarta "Allah ya kadarto auren na farko ba shine mijin ba, a yanzu da Allah ya yi haka sai nake gannin take takensa, ya ki yarda da abinda nake son nuna masa, ina yi masa gudun yace zai nuna zuciya da girman kai a wajen da bai dace ba, shine nace zan zo na sanar sai a yi abinda ya dace" Ya idasa maganar wannan karron yana dubansu baki daya "Innalilahi, innalilahi, innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, wai YUSUF nawa? RAUDA tawa ta gidan nan? SO? wani irin SO ?, kai, Ni du na rikice, wai tsaya kana nufin YUSUF na nan?" Hajia ke fada da mugun mamaki tana tafa hannayenta da tarin tunanin kai ba wanda take tunanin bane Murmushi SHAHEED ya iya yi yana sada kansa Ido ta karra zarowa ta dubi Mah yana fadin" Andiya kin ji wani salamamen tashin hankali? Yanzu yana son nata yana kallo yana ji ya yi shiru har wani ya shigo ya dauka? yau da ace tana cen da yaya zan yi? innalilahi yau ga wani abin mamaki abin rikicewa, to wai dama haka abin nan yake? to ita fa ta sani ne ko bata sani ba? ita din tana son sa ne?, koda yake ai ba zancen tana sonsa, jikana ko y'ar waye idan ta gani ai zata so walahi talahi ma kuwa, kai ai ka gama d'ana Allah ya saka maka da alkhairi aure an yi an gama , ka san ba komai ke wahalar da MALEEK ba sai jinnin nan naku na sarauta, shi ya fi yi masa ila fiye da kowa dan kuwa kana ji kana gani ka yiwa kanka ila dan wani dalili naka ai bai dace ba, kai subahanallah ashe haka ake yi ban sani ba? ikon Allah ikon gaske, ALLAH ya saka maka da alkhairi, wannan zance ai faduwa ya zo daidai da zama tunda har gobe take fita sai ta sake daukan igiyar daraja, dama zuciyata a kulun dokawa take yi saboda abinda na jajibo masa, shikenan yanzun alhamdulilah!" Duk irin farin cikin da suke yi Mah bata furta ko A ba,domin shi din da kansa Shaheed murmushi yake yi na farin cikin abinda yayi tunani ya tabata, dama ya san in dai Hajia ta ji an gama, duk wani na gidan mai yi mata biyayya ne, sai dai Hajia na kai kawo sai tafa hannaye take tana murna, shi kuwa yana shirin yi masu salama Mah a tausashe ,kanta a kasa ta furta " SHAHEED zauna, inada magana" Daga shi har Hajia sai da suka kalleta basu shirya ba Hajia da ta dauko waya ta dawo ta zauna tana dubanta ta ce" Andiya lafiya? yannayin nan naki bana so,me aka yi ne?" Mah ta sake sada kanta, kafin ta dago tana duban Hajia a tausashe ta ce"Hajia,Ni na jima da tunanin haka, harma na gane eh haka din ne, ama matsalar ita din ai bata son shi Hajia" Hajia ta tsura mata ido kamar tana son gane mutun ce ko aljan, a hankali ta ce" Ka ji wata bidi'a kuma, shi YUSUF din nawa ne ba'a so?, dama kin san da shi yana son yarinyar nan kika ki sanar min Andiya? me na maki da zafi haka?, kika kyaleni na je nake rarume rarume har na rarumo mai saka farcen matatu na aurawa bawan Allah?, haba kema Andiya to so meyema so din Allah na tuba da ake yiwa Yaren auren so din su je zama ya gagara?, ai sa so junnan nasu idan suka zama miji da mata, kuma Ni na tabata yarinyar nan zata so jikana, tana da wanda ya fi shi ne? meye aibunsa? Gaskiya Andiya ki daina wannan maganar haba , ko wani abin kikeda a rai sai ki bari ki huce a kaina Ni,ama ba a wajen da zan gaza dauka ba gaskiya!" Kai Shaheed ya sake sadawa yana adu'ar Allah ya sa kar Mah ta kawo wani tsaiko a lamarin nan,sai dai kash tun bai gama adu'ar ba ya ji a tausashe sosai Mah kanta a kasan nan tana fadin" Ba hala bane Hajia, babu wani abin dake zuciyata, gani na yi yarinyar nan yar amana ce, kuma sunnanta bazawara yanzu, hakan na nufin tana da damar zabar mijin da ya yi mata ba a yi mata zabe ba, kuma ni na tabata bata wani sonsa, a yi hakuri kawai ya yi zamansa da matarsa, dukama yaushe ta tare? idan ya so daga baya abinda hali ya bada sai a yi in sha Allah, Ko shi din, ko waninsa " Hajia ta sake zuba mata ido, sannan ta dago ta dubi Shaheed wanda ya gama ayanawa kansa ta faru ta kare, Hajia kuwa a yau harda mamaki sai da ya kamata na Mah, dan zata iya rantsewa tunda suke bata taɓa ce mata fari, Mah din tace ja ba sai yau Itama muryarta a tausashe wannan karron ta ce" AMEERAH, kina nufin ba zaki bamu auren y'arki ba dan bata son mu ko me?, kina nufin wani za'a kuma daurawa yarinyar da YUSUF ke so?, Ke fa kika haifi YUSUF , inace ko me yake so, ko a ina abinda yake so din yake ke mai zuwa ki nemo ki bashi ce, sai kawai in ga wannan abin kuma?, mu da aka mana auren hadin mutuwa muka yi? mu mazan basa son namu ma aka basu, muka rayu lafiya bale ita da ake so?" Mah ta sake yin iya yinta ta budi bakinta wannan karron ta dago tana duban Hajia a tausashe ta ce" Hajia, ke uwata ce, kuma ke kakar RAUDA ce kamar yadda kike ta YUSUF, na san a hada din ba komai bane, sai dai ki min uzuri ki bani dama har su kawo kansu da kansu, idan suka ki za'a kuma daura mata wani shi kuwa ya yi ta rike bakinsa, dan in har yana so din zai magantu ko wani irin jinni ke yawo a jikinsa, dan Allah ki yi hakuri Hajia " Ta idasa fada tana sada kanta, ta dan yi jim kamar yadda wajen ya yi dif, sannan ta mike jiki duk a sanyaye ta yi gaggawar guduwa dan bata san abinda zai je ya dawo ba kuma, abinda ta sani daya ne, ta shirya ja da kowa a kan maganar nan, babu wanda zai lalata mata amanar da ta dauko dan son zuciya, idan suka duba zuciyarta ta fi su murnar abin nan in dai haka din ne, sai dai ba zata so ta yi shi matsayin hadi ba, ita da kanta zata so ace ta samu SARAKUWAR da hankalinta zai kwonta a kanta, ba zai Amnah ba, Amnar nan tana tafe da kalar rashin da'ar da bata san a inda zata yi waje ta ajiye ba, abu daya tak ta sani ita da ita idan hanya ta hado su su san yadda hanyar ta ishe su, bayan wannan babu wani abu da zata nema na hadi tsakaninta da ita, dan ta kwatanta nuna mata daraja ta nuna bata san haka ba! Tunda Mah ta mike ta fice a falon wajen ya dauki shiru, shiru mai girman gaske wanda har sai da shaheed ya ji mugun nauyi ya kama shi da tunanin dama Mah din ya samu kafin Hajia ta ji, dan shi bai taba tunanin Mah zata ji abu mai mahinmanci irin wannan amsa irin wannan ta fito daga bakinta ba, bai san dai abinda ya sa Mah din ta fadi haka, kuma shi bashi da shedar eh lalle RAUDA na mugun son YUSUF, abinda ya sani shine amsar da ya gani a wayar YUSUF amsa ce ta idan an damu da kai, sai dai bai sani ba har ina girman damuwar ta kai Ajiyar zuciya Hajia ta sauke jikinta a mugun mace tana duban Shaheed ta ce" Ka san me yarona? ban san yaya zan yi ba yanzu, dan daga Ni sai Allahna na daukarwa kaina alkawarin daidaita mu'amalata da AMEERAH, inada damar daga hankalin kowa a gobe gobe a daurawa yarinyar cen aure, sai dai wani abu nace min kar na yi haka, ya dace in bata damar ta itama, dan ta nuna tana son a yi adalci kuma ta nuna ba za'a hanna mana yarinyar ba ko?" Murmushi ya yi yana duban Hajia, dama shi ya san akoy ranar da irin maganar nan zata fito daga bakinta a kan Mah, lokuta da dama idan suka samu matsala ita da YUSUF a kan Mah yakan ce masa ya koyi kawar da kai a cikin lamarinsu, ya ringa tausasa Mah, in sha Allah duk wani abinda ke rikita masu lissafi zai daidaita, Mah zata ji dadi fiye da tunani dan a yi hakuri a bari Allah ya daidaita abinsa ya fi ace za'a yi garaje A tausashe ya furta" Ki yi hakuri, ki yi addu'a, ki kuma kamanta tayawa, daga wannan idan har wani ya kuma fito mata ba shi ba ki yi hakuri cen dama ba shine mijinta ba!" Hajia ta hadiye yawun dake wuyanta tana tunanin zata iya kuwa? jiki ba karfi ta yi masa rakiya, sunna tatauna maganar har wajen get na farko sannan ta juyo tana ta sake shawara da komawa kan shawararta ta farko, bata san in har ita zata iya hakuri tana ji tana ganni a yi haka ba, sai dai Shaheed ya fada mata ko me za'a yi ba za'a tsallake hukuncin ubangiji a kan lamarin ba, ya kuma fada mata adu'ar itace ta fi fiye da tada zaune tsayen...., da wannan ta karasa ta shige bayi saboda kiraye kirayen sallar magariba da aka fara. Kwonci tashi asarar mai rai Yau RAUDA ta wayi gari cikin wata sabuwar rayuwar da ta sake sakata a halin tunanin yau da gobe kafin ta dangana ta ajiye gefe saboda mutanen dake zagaye da ita tamkar ana yin wata sabgar ne Tunda safe Atu ta sauka a gidan, Salima kuwa duk kin da ta yi sai da ta kunsa mata kunshi dan Hausa harda yan yatsunta sannan ta amso dinkunnan da aka yi mata tace a gobe sai ta saka, ko da safiya ta yi da ta yi wanka a dole ta sa ta saka suturar ta yafa mayafi ta zauna tare da bakinta da yan gidan sun mike a fira, Bah ya yi kira cewar ta zo su yi salama da Uncle dinta, dan a yau yau zai daga zuwa kasar waje dan neman lafiyarsa kamar yadda MALEEK ya sanar masu, kuma kiran da aka yi mata bangaren MALEEK din ne zasu je dan su Bah din sunna cen tare da uncle Umar da likitan da zai yi masa jagora har zuwa ƙasar wajen, kasancewar yau Asabar bai fita ba , sai suka same shi a cen din gaba dayansu Hijab ta so daukowa, sai Mah ta nuna mata mayafinta bashi da wani laifi, sannan ta nuna ATU da Salima su yi mata rakiya Har zata fita a dakin Mah, Mah din ta yi kiranta, ta mike ta dauko turare ta karaso ta shiga fesa mata fuskar nan tamau a hade danma kar tace a'a, sai da ta yi mata wanka da shi sannan ta umarce ta kan ta je, ta juya ta fita tana waiwayan Mah din, domin tun jiya da dare ta ga yannayinta wani iri, kuma ta yi ta tambayarta amsar daya ce lafiya kalau , ba komai. A nutse suke takawa, tana bin gine ginen nan da kallo, dan rabonta da ta karewa wajen kallo tun kaurowarsu da gabanin aurenta, tunda ta shiga takaba kuwa bata tako ta nan baban filin gidan ba, ta dai fita ta cen baya zuwa bangaren Hajia, sai yau da suka fito ta ringa gannin gidan sai karra kyau yake sanadiyar shuke shuken da aka zuba ta ko'ina, flawowi ne da shuke shuken fruits kala kala, du sun fara tasawa gidan ya fara daukan Color na shuka masha ALLAH tafia suke yi a nutse, a jikinta dinki ne na lesh fari kal mai dan digo digon somon sai dan kyalkyalin da ba za'a rasa ba, an yi mata ɗinkin sket da riga budadiya ama bakin tsayin rigar gwuiwarta dan sam bata sauka kasa ba, hannayen ne a bude sosai sai wuyan da aka yi irin baban wuyan nan da baya yiwa ramamu kyau ta yi daurin dan kwalin da ya fitar da gashinta sosai ta baya, sai mayafin da ta yafa a saman kanta, mayafin kuwa shara shara ne sosai, hannayenta ba komai dan ko wayarta ta baro a dakinta,, sai takalmin da ta saka plat mai tsadar gaske Sunna daf da shiga get na farko bayan sun gaisa da sojawan dake kofar baban sojan dake ja gabar masu tsaron wajen ya zuba mata ido da kallon da har sai da su Atu suka ankara da shi,, ama ita ta yi tamkar bata ganshi ba, dan ta riga ta tsarawa kanta soyaya kuma ba dai kwana kusa ba gaskiya, shi yasa ta dauke kai a lokacin da Atu ta ce" Shi yasa ta dauke kai a lokacin da Atu ta ce" Ama gayen cen ya iya kallon kurula, ji min mutun, ta yiwu kowa idan ya zo sai ya kure shi da kallo haka" Salima ta sake waigawa da sauri ta dauke kanta dan ita tsoronsa take ji tun ranar da suka zo rakiyar Amnah kiri kiri ya hanna masu busa shiga, kuma yan rakiyarma sai dai da daidaya aka ringa shiga ana fitowa, irin yadda ya tsare gida a ranar harta manyan sai da suka tsorata, yau kuma shine da kallo irin wannan? "Uhum, wancen? barshi inda kika ganshi, walahi mugun miskili ne, kuma baba ne a harkar soja, kin san shi ke jagorar sojawan gidan nan kaf, Ni tsoro yake bani, Allah ya sa kallon da yake yi din ba na ya koramu bane!" Jin haka ya sa RAUDA jan birki, itama ta juyo ta dube shi kamar yadda ya dan mike daga tsayuwar da yake gannin ta tsaya kuma har ta dube shi har ga Allah ya san a aikinsa akoy kiyaye irin abubuwan nan, bale a wajen da yake shi ke hanna yarensa shagalta da komai da gindaya masu sharudan ba su ba bibiyar yan matan gidan koda barori ne bale ya'yan gidan, sai gashi yana ji yana gani kaffafuwansa na sake matso shi har ya samu kansa da tsayawa dan nesa kadan da ita yana sake yi mata kallon da ya wuce ka'ida yana gannin yadda Salima ta sake tabatar masu ta tabata kora su zai yi, ya kasa ce mata ba kora su zai yi ba, karra kallon wannan halita dake gabansa zai yi koda kuwa ya san hakan na iya jaza masa yin nesa da aikin nan mai tarin ni'ima Murmushi ya yi ya ce" Yan matah....., bakuwa ce ke ko a nan kike?" RAUDA ta lumshe idannuwanta tana jin tamkar ta yi wani mulmulalen ashar, dan har ga Allah sai ta ga ana neman wulakantata ne a wulakanta takabarta, duka duka yau fa ta gama ko? shine har za'a samu wani dan balaja'un da zai tsayar da ita? Takaici ya sa ta juya bata tare da tace da shi ci kanka ba ta nufi ciki Da dan sauri ya dubi Salima da mamakinsa ya gama kasheta yana fadin" Kanwata, dan Allah ke ki saurare ni" Salima ta yi murmushi tana kallon sa Shima sai ya rasa me zai ce, ta inda zai fara, abu daya ne ya sani yana kallonta ya ji ta gama yi masa dari bisa dari, dan kuwa ya ga halitta gannin idannuwansa Ajiyar zuciya ya sauke yana hangen ta kama babbar kofar falon ta bude ta shige a raunane ya furta" Ina son ta!" Salima ta dan zaro ido, ba dan komai ba sai jin muryarsa ta cenza daga yannayin karfi da umarnin jiya, zuwa laushi a yau Murmushi ta yi, ita kuma hankali kwonce ta ce" Ka tabata da gaske kake?" Ya yi murmushin shima yana kallonta ya ce" Ta fi karfina ko?" Salima ta dan baza hannayenta tana sake kallonsa ta ce" Ya danganta, da wani irin mutun ne kai, idan har kai din namiji ne da ya iya son mace , da kuma da mace, to tabas zan iya baka y'ar uwata, ama kafin nan ka fara neman izini wajen Bah baba idan ya baka an gama " Tana gama fadi ta juya tana murmushi ta yi ciki, shi kuwa ya rasa fargaban maganar ya tambayi uban gidansa maganar nan zai yi ko kwarin gwuiwar tunkarar uban gidan nasa saboda ta cencenta? abinda ya sani daya ne yarinyar nan ta isa a cikin isasu tunda har ta iya dukan zuciyarsa a gannin farko, ashe y'ar gidan ce? ya rab ka sa abin ya zo min da sauki A lokacin da Salima ta karaso, ATU na tsaye bata shiga ba, hakan ya sa ta kalli hanyar da ta tabata a irin yadda RAUDA ta yi gaba da zafin rai yaci ace ta shige tuni Idannuwanta suka sauka a kan RAUDAR a tsaye, hannunta rike da fari kal din labulen falon, idannuwanta kuwa a risine tamkar wace ke kallon wani abu ko ke gudun kallon wani abin Kasa kasa ta ce" Menene? lafiya?" ATU ta sauke ajiyar zuciya tana jin tamkar ta gudu, sai dai ta san ba damar guduwa A cikin falon kuwa, tunda Rauda ta bude dakin nan da yannayin garaje a zuwanta na bakuwar wajen wace bata taɓa ziyarta ba, ko a yau din ta bude din ne dan Salima ta tabatar mata cen din shine baban kofar falon baba na bangaren gaba daya, sai ta ji duk irin sanyin wajen yana neman zame mata zafi sakamakon gannin wata rigar alfarma sakale da jikin alfarma daga barin hagu mai dan tazara an dan bude labulen wajen ana tsaye ana kallon baban filin get din na biyu na dogarai, wanda ke tabatar mata duka kaf abinda ya wakana yanzu an gani, hakan ya sa ta kasa karasawa cikin falon take tsaye da burin jin an maidata baya dan ta riga ta sanyo kanta cikin, sai dai aka yi kamar ba'a san da ita a wajen ba, aka yi kamar ba'a gane ta shigo wajen ba aka ci gaba da kallon abinda bata san ko menene ba, har sai da Salimar ta karaso kasancewar bata dauki lokaci mai tsayi ba ta gaza tsayawar kawai ta kama hannun Atu tana fadin" Mu je mana aminiyar mu" Suka shigo su dinma, sai dai su sunna shigowa Salima ta nemi zubewa saboda wanda RAUDA ke tsaye tana kallo su dinma sun ganshi A nutse ya juyo da jajayen idannuwansa ya sauke a kan fuskarta Tun daga sama har kasa ya sake bin suturar jikinta da kallo da mayafin dake jikinta Kansa ya dauke ya nufi falon da su Bah ke shan fira shi da abokinsa wato uncle Umar, dan alakarsu a yanzu tana da karfin gaske A hankali ta ringa fitar da numfashi daga hancinta, kasa kasa ta ringa kallon su SALIMA Idannuwanta ta lumshe ta masu alamun su je SOSAI Salima ta so juyawa, ama ta kasa saboda rikowar da Atu ta mata ta nuna mata tare fa zasu je din walahi sai dai kowace wace sunna karasawa Bah ya tarbe su da fara'a yana masu sannu yana kama sunnan daya bayan daya, haka uncle Umar Zama suka yi a saman kafet su dukansu, a lokacin ne kuma Amnah ta sake zuwa dauke da wani plate din kayan baki ta sake ajiyewa, Bah na yi mata adu'a ta juya, ama idannuwanta sun sauka a kan wace take hako da burin samun yancin da take bukata dan birkita duniyarta!, hakan ya sa ta kasa komawa sai kawai ta labe a kusa dan jin komai a kan wannan karamar y'ar barikin Tun da suka zauna din ake yi masu nasihar baki dayansu , kowace an yi mata nasihar dai-dai da abinda ya dace a yi mata har Bah ya zo kan RAUDA A tausashe, bayan ya tuna maganar da suka yi da Hajia ya sauke ajiyar zuciya kuma ya dan kalli YUSUF din ya ce" Y'ata, ba zan gaji da baki hakurin rashin miji ba, ki yi hakuri kin ji? idan mace ta rasa miji ta yi baban rashi a rayuwarta mai matukar wahala, sai dai idan kika yi hakuri kika yi ta addu'a Allah zai fido maki wani, dan a cikin goma dayama baki dauka ba, kuma na san babu wanda zai ga y'ata ya kita, shi yasa zan karra maki nasihar ki kula da tarbiyar ki da darajar ki ta y'a mace, har Allah ya fitar maki da wani mijin na sake bashi amana, a yi ta hakuri da rayuwa kin ji?" RAUDA ta sake sada kanta tana sauke ajiyar zuciya, a hankali ta gyada kanta dan ba zata iya budar bakinta a irin wannan adu'ar mai girma ba, ko ba komai iyayenta ne, akoy nauyi sosai tsakaninta da su, shi yasa Salima ce kawai da Atu ke amsawa, su dinma ba wai da wani karfi da iya yi ba, a hankali cike da kunya Uncle Umar na murmushi shima ya dora tasa nasihar, ya idashe da fadin" Kin ga lokacin tafiyarmu ya yi, ki ci gaba da yiwa iyayenki adu'a na san ko na mutu yau hankalina a kwonce yake a kanku ke da d'an uwanki, dan Allah tunda kin samu kin fita a takabar ki je ki dauko shi wajen mahaifiyarsa,, na fi jin nutsuwa idan yana tare da ke, dukkan wata nasiha ta kirki kina samu RAUDANA, fatana ki ci gaba da dauka har karshen rayuwarki, Allah ya maki albarka" da amen suka amsa, banda shi dake zaune da tanfatsetsiyar samsung dinsa yana dubawa A nutse ya daga waya, ya dan yi shiru kafin ya ce" Ok docter gasunnan, A sauka lafiya " Daga haka ya dubi wajen Bah, wanda ya mike yana fadin" Malan Umar mu je, likita har ya isa aeroport ko?" Kai ya gyada yana kallon su, sun mike su duka da kuma gagawa suka fice, hakan ya sa mikewar da yan matan suka yi basu kai ga fita ba ya rufe kofar ta hanyar aiki da abin rufewar dake ajiye saman karamin teburin wajen sannan ya sake dagowa yana duban Salima wace ta dawo ta duka dan ta fahimci magana yake son yi Kasa kasa sosai ya furta" Me yasa kuka fito ta nan bayan ga hanya nan ta baya?" Salima ta yi saurin kallon RAUDA, wace ke tsaye nesa kadan da su, ta sada kanta ta ce" Yau RAUDA ta fita, shine muka fito ta nan dan ta dan rawata kafarta " "A part din Mamanta babu abinda babu na rawata kafa, ta rike kaffafuwanta iya cen, i'm i clear?" Salima ta yi saurin gyada kanta tana tunanin me kennan?, sannan ta nemi izinin tashi daga tsugunnen ? Sai dai me, bata kai ga tashi ba, wani gigitacen shedani ya turo RAUDA, RAUDA dai tasu mai sasaukan hali da biyayya ce ta karaso saman kafet din nan, kaffafuwanta masu ɗauke da Safa ruwan ash mai kwaliya ta ringa lotsawa a saman kafet din har ta karaso dan daf da kujerar da yake zaune yannayinta idan ka kalla zaka gane tana dauke da magana irin ta bacin ran nan, ama kuma ta danne A tausashe tana kallon sa kamar yadda ya zubawa fuskarta ido yana kallo ta dan risina dubanta kadan a hankali sosai ta furta " Da tace na fita, tana nufin na gama takaba....hakan na nufin Dole zan fita ko dan Allah ya bani wanda zai kuma daukewa duk wani wanda na zamo jidali a idannuwansa Ni, Allah ya huci zuciyarka Bah karami...... Ni RAUDA ba akuyar dauri bace!" Daga haka ta mika hannu a inda abin rufewar yake, tana jin ranta na tafarfasa da tabbacin ko waye shi walahi walahi ba zata taba yarda ya rikita mata lissafi wannan karron ba, wancen sojan kuma zata je ne da kanta yanzu ta amshi numbarsa, idan soyaya ya zo da ita zasu yi sai me, tace sai me?! Sai dai a lokacin da ta dora hannunta a kai, a lokacin Salima ta baje a kasa tamkar an watsa mata mari, Atu kuwa ta dora hannayenta saman kai ta je ta liku da kofar fitar tamkar kadangaren dake neman ruwa , a lokacin ne bata yi zato ko tsamani ba, bata taɓa kawowa kanta ba, batama gane ta yaya duk girman jikinta da kamewarta ba, ta jita tamkar an daga yar farar leda ba karfi an kuma zaunar da ita saman kujerar da babanta ya tashi, lokaci daya an cire rawanin dake dan sakawa ana dan yin nesa da idannuwan nasa, da kuma yannayin fuskarsa, lokaci daya tak aka tunatar da ita karfi ba dayya, ba,, kuma karfin murya ba daya ba, a lokacin da ya kama fuskarta ya dago da karfin da ya sa ta bude idannuwanta ta zuba cikin nasa, a lokacin ne kuma matarsa ta fito da gudu ta dora dubanta a kan haka, a kuma lokacin ne ya budi bakinsa Rai bace, ido cikin ido yana dubanta a kausashe ya ce" 😭😭😭😭😭, Ni wollah ko, to wai ma to wai kam.. a dai ringa amsar BONANZA 😂😍😍😍 Azl 51 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo A kausashe sosai ya furta " Kin cika wasa da abinda yake iya dauke numfashin ki!, kina so ki sake nuna garaje a tafiyar nan!, Ke ba zaki iya yin biyayya bane?, Bana tunanin zaki iya kokowar, ba ke ba ko wani yace zai ja da wahala ya kai, kar ki sa a sameni ta hanyar ki!,, nace ki bi ta baya, ki zauna a cikin daki shine umarnina, shin zaki yi ko a'a?" Tunda ya fara magana hawayenta ya bale, kuka take yi ama ba mai karfi ba, Sai dai bata sani ba ita hawayen ne ke zubowa dan kansu, bayan na Amnah da karfin tsiya suka bale mata bayan ta dora hannayenta saman kanta tana kallon abinda zata yi kira da baban tashin hankalin da ba zata taba cin karro da irinsa Bama bale ace ta taɓa cin karron da irin nasa ta shiga a halin firgici a tsayen da take hannayenta saman kanta tana kallon mutumen da ya zame mata zinari cikin kasa ko ganninsa ya zama aiki bale riko shi rike da habar wannan da ta dauka kaskantaciya a cikin kaskantatu yana yiwa kashedin da ba zata so ta san dalilinsa ba, abinda ya sakata kuka ba wani bane, dama kusancinsu ya kai har ya taba habarta? a shigowar da ta yi gidansu har ta kai matsayin da haka zai faru ita da shi?, menene ta yiwa mijinta da ahalinsa da suke sonta? menene darajar da take da ita a duniya da har zata samu wannan damar? Salima da Atu kuwa tsabar firgicin abinda suke kallo ya saka Salimar langwabar da kai tana hawaye, hawayen da ba zata iya fadin na meye ba koda an dora Mata bakin bindiga a kanta, Atu kuwa sai ta ringa shafar yaron cikinta tana hade hannayen alamun bada hakuri ne ko meye?, ita dai gatanan kamar irin an saka mutun a ukun nan, dan basu tashi fara bin hanyar da ya nuna masu ba sai da RAUDA ta fashe da kuka mai kara tana buga kaffafu, hakan ya sa da sauri sauri gudu gudu suka kama hanyar bayan sun riko hannayenta sun sakata tsakiya ita kuwa tana karra karfin kukanta har suka isa falon Mah, wace ihun kukan ya sa ta fito da sauri tana kama sunnan RAUDA, a birkice ta ce" Baby, subahanallah lafiya? menene,me ya faru, ke da waye, ke Salima wa ya dakar min yarinya? ko faduwa ta yi!?" Salima ta samu kanta da yin tsuru tsuru,Atu kuwa da tarin takaici tana kallon RAUDA ta ce" Na rantse ki mana shiru ya rainin hankali na rantse ki kama mana bakinki ke da baki san lokacin yin rigima ba, yau da kika sa aka dakeni da sai na rama a kanki, fitsarariya kawai" Salima ta rafka tagumi, sai kuma ta dauke tana kallon Mah da ta ci gaba da fadan a fada mata wanda ya taba mata y'a!, ta ce" Yau dai, da tabas mun samu abinda muka je nema harda kari,ke yanzu haka kike? Ki duba ki ga mutanen dake kiransa Bah, dan yace kar ki biyo ta babbar kofa shine zaki ce sai kin biyo?Bah karami ne fa?" Mah ta yi dan tsai, a hankali ta furta" Dan kun bi ta babar kofa ne aka maku fada?" Salima ta gyada kai tana kallon Mah ta ce" Eh Mah, shine ita wannan uwar bacin tace wai ta fita ida ai yanzun, shine fa ta sa ransa ya ɓaci " Mah ta tabe baki tana mikewa hadi da kama hannun RAUDA ta ce" Mu je, tunda sunna gannin gaskiya suke son takewa, wuce mu tafi, zan yi kiransa da kaina mu yi irken kwanakin da kika dauka a dakan, ta yiwu yana tunanin basu cika bane, ama bayan wannan ai takaba kai kin gama kuma bi'izinillah fita ta babar kofa yanzu kika fara koda wani auren ya hau kanki bale babu, Allah na tuba yarinya karama da ke za'a sako min ke a gaba? walahi kowa ya ci kansa ko waye!" Da ido suka raka su, Salima ta juyo tana dafe haba ta ce" Kai jama'a, kamar ita wancen da mamanta sun dauko wani hali ko?" Atu ta saki murmushin da sai yanzu ta samu karfin gwuiwar yi, tana kallonta ta ce" ai kin san ko laifi gareta sai dai daga ita sai ita ta mata fada, yau da na san yan iskan kan Rauda har shi ba zata bari ba da ban bita ba, na tsorata ainun, ama kuma MALEEK akoy karfi ke ji walahi da ya dungumeta ya ajiye kamar bai yi wani yunkurin daukan balagage ba, Allah dai ya takaita fitinar nan dan Ni ban cika son neman rigima ba" Salima ta girgiza kai tana kallonta ta ce" Ba zaki gane ba, kin san duk wani abin dake kanta, walahi yana kansa, kin ganshi nan baya tsoron kowa, sai dai daga kafa da kuma umarni idan ya zame masa dole, ama a kan lamarin ta ina gannin abubuwan da nake fatan gannin karshen game din, " Atu ta yi shiru, tana ta sake saken dake ranta, itama Salimar tana ta tuna sakon nan na wayar RAUDA, .....kai da abu nasu maganin a kwabe su, da ta fi kowa farin cikin hakan walahi A bangaren YUSUF tana barin wajen da su Salima ya zauna a saman kujerar yana daukan mayafin nata da ta bari a nan ya jimke a hannunsa sannan ya dago yana kallon Amnah da wani irin kakausan kallon da ya sakata zaunewa a wajen kanta a kasa ta kasa hanna kanta kukan nan A birkice ta dago dubanta tana kallonsa, muryarta a raunane sosai, da yannayin tashin hankali ta karyar da kanta sosai ta ce" Ni kam, kamar wata wace take da kusanci da kai fiye da tunanina?, inace Mah ke rikon ta, Bama y'ar Mah din bace ko?, kuma Ni na san ba dai maganar soyaya ba, ba dai da ita ba walahi, dan Allah daukanta ka yi fa ka ajiye kuma ka kama fuskarta da hannayenka masu daraja, ka san girman darajar hannayenka kuwa....., Haba MALEEK......." Ta idashe tana fashewa da wani kukan dan bata taɓa tunanin za'a wulakantata haka a rayuwa ba, kuma abin mamaki wulakancin ya sameta kai tsaye ta kasa yiwa abin rashin kunya, saima wata sabuwar lalabawa da take bin abin da shi a kan dole , dan ta sani tunda ta yi tsaye a gabansa ta gane mijinta ya gama dameta a duk wata kiririta da take tunanin tana da ita Idannuwansa ya dauke a hankali a kanta, bai iya ce mata ci kanki ba ya lumshe idannuwansa dake masa zafi, a hankali yana sauke ajiyar zuciya Ta jima da jiran tsamanin jin bayanin dalilin da yasa ya taba RAUDA, ko ya dan rarasheta ko dan kukan da take shekawa , ama fir ya murje tamkar baya wajen har sai da ta mike da kanta ta nufi nata part din bayan ta gama gane bata haife shi ba, ba zata titsiye ba kennan!, ya ilahil alamina, jikinta zafi ya ringa dauka na tashin hankali dan haka ta dokawa mahaifiyarta kira tana zaunawa kasa jikin gadonta tana ta murzar fuskarta ta shiga yin bayani da ita....... A falon kuwa ya jima yana hanna kansa magana ne dan kawai irin zafin dake saka masa tunani kala kala a kan wancen sojan........abu daya tak ya sa ya zauna din nan har sai ya gama samun nutsuwar zuciyarsa kafin ya dauki mataki dan girman da aka kakaba masa rana tsaka, ya sani a yanzu idan ya fita cen ya ketsawa wancen mari koda ba'a ce masa komai ba sai an baza shi duniya saboda wannan, shi yasa ya yi zamansa sai da ya samu ya dan sauka kadan sannan ya yi kiran uban gidansa da ya bashi shi ya sanar masa a dauke shi bai san aikinsa ba sannan ya katse kiran ya mike ya nufi Part dinsa da mayafin nan ya je wajen tufafinsa ya bude yana kallon wasu jerin abubuwa harda abin hannu wanda aka cire mata ranar da suka yi accident, harda mayafinta na ranar nan, a hankali ya ninke wannan dinma ya saka shi ciki sannan ya karasa wajen gadonsa ta baya baya ya fada yana rintse idannuwansa da karfi dan magance abinda ke masa yawo a idannuwan......a saman lebensa ya furta" Mai kukan banza kawai, sai neman fada ana zaman lafiya, kina tunanin zan kyale ki ki kasheni ne? dilla ma malama!" kwana biyu tsakanin wannan rikici nasu Mah ta aiki RAUDA cikin garin Damagaran, kuma aiken Mah ta hanna direbansa ya kaita, ta sa wani direban cikin direbobin gidan ya kaita, ta bata damar ziyartar duk wanda take so, wanda suke zumunci, ta bata kudade masu yawa koda zata yiwa wani kyauta, ama ta kula da mutuncinta Baban tashin hankalin irin kwaliyar da ta sa ta dauka ita da kanta zata iya rantsewa tunda aka haifeta bata taɓa saka sutura mai tsadar nan ba, kuma bata taba hauda jaka da takalmi da mayafi masu kudin nan a jikinta ba, haka kuma bata taba Hauda siririyar kwaliyar da ta fitar da asalin sirin kyan fuskarta irin na yau ba, dan mai kwaliyar nan ce ta zo har gida kamar kwaliyar amarya jama'a ko ta bikin sunna ta yi mata abinta har a daki, sunna yi sunna dariya ta yi mata siririyar kwaliyar da ta matukar birgeta, kuma ta kafe mata dauri dan daidai da kanta ba mai hayaniya ba,...kai kwaliyar kwaliya ce har kwaliya walahi, tana gama mata ta watsa mata hotunna da vidio ta shiga karra gyara su kamar yadda ake yi, dan harda Mah sai da ta yi mata sau uku sannan suka tafi ita kuwa ta yi tsaye saman turaran wutar da Mah ta saka mata yana bin jikinta tana karra jin gargadin Mah, kar ta yarda la'asar ta yi mata a cen, ta juyo da wuri, kuma ta kula da kanta , Allah ya tsare Wayarta ta dauka ta fice, mayafin tana jin kamar girmansa ya yi mata ƙadan dan bashi da wani girma, ta karasa wajen wawatsetsiyar motar da aka parker ta bude bayan ta shiga, direban na zaune ya gaisheta da girmamawa, shima saurayi ne da ya san aikinsa sosai, ta amsa tana fada masa inda zasu fara zuwa dan amso sakon Mah din kafin su wuce tsohuwar anguwarsu wato gidan Mama, sannan su je ta ga Abdul , sai gidan Atu shikenan yawon nata , ta daga wayarta tana sanarwa Salima ta fita, sannan ta bude datar ta ta shiga kale kale hankali kwonce har suka gama fitowa a gidan suka dauki hanya Sunna ta tafia , sunna daf da isa gidan yayar Mah mai kwaliya ta tura mata hotunan nan, ita kuwa tana budewa tana murmushi ta turawa Mah su gaba daya sannan ta yi kiranta ta sanar mata ta tura mata hotunan, kuma har sun iso gidan aunty baba Mah dake falon Hajia tana murza mata kaffafuwanta dake ciwo saboda yau ta tashi da rashin lafiya , hakan ya sa YUSUF sanarwa Mah din, dan yana ɓangaren Hajiar sunna firar wasu filayenta ya ga sosai ƙafafuwan na damunta shine ya sanarwa Mah dan ya tabata ba za'a rasa magani ba duba da itama ciwonta kennan kafafu Tana murmushi ta mika masa wayar ta ce" Dan bude min wajen sakon baby ta turon hotunanmu da aka yi mana yanzu kafin ta fita , bude min in wanko hanuna in gani" Ta fada tana mikewa ta rufe maganin ciwon kafar ta nufi bayin dake falon dan wanke hannu, shi kuwa ya dan yi jimmm, jin ta ce ko kafin ta fita? fita ta yi? zuwa ina? Baki ya dan tabe ya shiga bude hotunan harda vidios din, sai dai bai idasa budewar ba ya ji tamkar ciwon nan na hawan jinni dake sangaye bari daya na jikin mutun ya sangaye masa zuciyarsa, kafin ya saketa da karfin gaske ta ringa bugawa da mugun bugun da ya saka shi saurin rintse ido gumi na tsatsafo masa "In gani?, sun budu ko?" Mah ta fada tana kallonsa Yannayin da ya dago yana duban Mah ita da kanta sai da ta ji karsashin da ta fito da shi na neman barinta, Hajia kuwa lokaci daya ta dube shi tana fadin" YUSUF lafiya?, subahanallah, meye kake haki?" Gannin numfashinsa na iya barin gangar jikinsa a zaunen nan ya sa ya ajiyewa Hajia wayar ya mike ya fice ta babar kofa da saurin da ya sa Mah wace ta zauna mikewa a birkice tana kiran a kirawo mata shi, dan fitowa ta yi da sauri din, ta saka dogarin dake wajen bin baya da gudu, sekwani kadan ya dawo da sauri yana dukawa ya sanar mata cewa ya fice a mota hakan ya sa ta koma dakin hankali tashe tana kallon Hajia ta ce" Hajia dan bani wayar na yi kiran baby" Hajia ta dago tana dubanta rai bace ta ce" AMEERAH, bari ki ji, kar ki yarda ki bata rawarki da tsalle, macen da ba'a so ake taya jajen an mikata dakin miji ba wace ake so ba, kuma sarauta ba karya bace, bayan sarauta hali ba karya bane, ban cika ba wani abu wai shi so mahinmanci sosai ba, ama har Ni nan na ziyarci zana'izar yan soyaya, ki kula, ki kula Ameerah, kina neman yaron nan da lafiyarsa ne, fitar nan da ya yi Allah ya takaita rikicin da ake iya yi, saboda wannan kina fushi da mijinki kwana hudu kennan dan yace za'a daura auren, babanta ya nuna bata da miji sama da shi ama ke kin nuna sai ta amince, ki sani a yau zan nuna maki Ni din ce na haife kin, dan zan baki umarnin da nake so ki bi dan na isa da ke, wayar nan da zaki amsa ki min kiran Bello da shi da duk wani wanda ya isa da shi a Daura auren nan, idan ya so in kin ga dama kya bashi matarsa, idan kika ki kar ki bashi, abinda na sani daya ne a yau sai an daura auren nan! (😨😨😨😨😨🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️) Azl 52 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo A kokarta a ringa amsar BONANZA TA NOVELS DINA ALL A BISA FARASHI MAI RAHUSA SU 22 CIF IN SHA ALLAH WATO 1K A TUNTUBI MAR'ATUSALIHA BISA NUMBANA KAMAR HAKA 93811618 Jiki a sanyaye Mah na kallon Hajia ta ce" Hajia yau?" Hajia ta sake dubanta cikin ido ta ce" Yau yau, kuma yanzu yanzu, ki kira min mijinki ki bani, tunda har wanda yake mahaifinta ya bamu, nake burin gannin abin ya kai inda muke so, kunyar ki da gudun bata maki ya sa na yi shiru ya koyawa kaina hakuri irin na kowa, ama a yanzu na kula, ana iya cinma mutumen da yake da nauyin jama'a a kansa saboda ana son sai an saka shi dole abinda yake iya hafmdiyewa har ya mutu da shi, kin ga ban hanna ki hanna masa ita ba, ban kuma hanna ta cewa sai an nuna mata so ba,cikar mace kennan ai jan aji, ama matar Sarki ta fi karfin tayawar talaka, ko bayan ransa in dai ta riga ta zama tasa sai dai kowa ya yi hakuri, ki yi hakuri Ameerah, ki yi hakuri" A sanyaye Mah kanta na kallon kasa ta ce" Hajia, Ni bani da ja da hukuncin ki, sai dai ita yarinyar idan ta nuna bata so fa?" Hajia ta yi murmushi tana kallon ta, a tausashe ta ce" Kina tunanin da irin ya'yan nan tsageru ne ita da na yarda ta zauna a gabanki? tunda ta zo gidan nan an gaya maki bana bin motsinta? dole zan bincike ta kar aje wani ya turo ta, yarinyar nan ta daukeki uwa, ko wani da ya rabe ki kika nunawa ta yiwa biyayya an gama bale ke" Daga nan Hajia ta yi shiru tana mikawa Mah hannu har sai da ta yi mata kiran Bah ta bata sannan ta mike da kyar ta yi cikin dakinta Zaunawa Mah ta yi a sanyaye ta sada kanta, zuciyarta na bugawa cike da wani irin tsoro na abinda ke iya zuwa ya dawo, ta san da wahala Rauda ta ƙi auren nan, sai dai ba RAUDA ta fi ji ba a yanzu kamar matarsa, kai ita fa yarinyar na bata tsoro Allah kuwa, ba zata so ta kai yarinyarta karama a wahalar ba, ba zata taba iya hakuri a cutar mata da RAUDA ba, a yanzun ma sai ta mike ta nufi bangaren su Salima dan ta amshi wayarta ta sanarwa baby su juyo duk inda suke, dan ta sani ya san inda take abu ne mai sauki koda bata tare da ma'aikatan sa, bale tana tare da direban dake aiki karkashin sa, bata so ya yi wani abin da yarinyar nan zata koma jin haushin sa , bata san a me ya dauki y'a mace ba, abinda ta sani daya ne yana iya shan wahala saboda so, dan ba kowace mace bace zata yarda wai da Yaren ido da hannu! A lokacin da Mah ta karasa baban falon Hajia ta yi ya salama, ama abin mamaki babu kowa a falon, hakan ya sa ta nufi karamin falon tana tunanin ko Hajiar na cen, dan ba zata iya shigowa ta nemi Salima ta fice ba tare da ta gaisar da ita ba A lokacin da Mah ta tunkaro karamin falon Hajia ta ringa jin magana da wani irin iya yi, da isa isa , da wani kalar takama, maganar ba muryar Hajia bace, hakan ya sa ta dan dakata sannan ta so juyawa dan bata cika son shiga sabgar kawayen Hajiar Salima ba, dan mutanen sam basa mutunta ta, sai iya bin mutun da kallon raini, A lokacin da ta juya din ne Muryar AMNAH ta shiga kunnenta, Muryarta da wani irin yannayi na bacin rai ne da cin alwashi ko menene? ita dai ta ji muryarta ta fara magana, yakan ya sa ta dan ja ta tsaya da mamakin dama Amnah na kawo ziyara nan ama bata kaiwa cen wajenta?, A lokacin ne AMNAH cike da wani gagarariyar magana ta ce" Ba zaki gane bane mom, bana tunanin akoy wani mahaluki da zan iya bari ya shiga tsakanina da mijina!, kin ga ki daina min maganar wancen gawa ta ki ramin dan walahi ni a mataciya nake kallonta matar nan fa kusan kulun sai kin ji an ce wani ciwon nata ya tashi, lokaci dai ama na tabata zata yi gaggawar Bara min d'anta in yi yadda na so da abina, dama dama wannan masifafiyar kakar tasa, itama zan san yadda na yi da ita, dan wahali sai na maida ita mahaukaciya tana ji tana gani, abinda yasa nace ki zo yarinyar nan da ya dauka nake so a batar, mom ba zan iya kuma tunani mai kyau ba in dai tana doran kasa, a batar da ita dan ta shiga abinda bai dace ace ta shiga ba, ko ni da yake aure bai dauka ya ajiye ba sai ita? ba zan iya hakura ba, ba zan iya yafewa ba mom!" Ta idasa tana dantse lebenta, hakan ya sa Mah zarro ido, jikinta ya dauki rawa, tashin hankali ya ziyarce ta har ta so gaza taka kaffafuwanta sai da kyar fa sidin goshi ta iya juyawa ta nufi hanyar fita kirjinta na dokawa fiye da kima Da kyar ta kai kanta falon ta, tana zuwa ta zube saman kujera tana cire hijab dinta jikinta na rawa tana jin kamar ciwonta zai tashi "innalilahi wa inna ilaihi raj'une" Azl 53 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo Mah ke fada jefi jefi a hankali, har bata san shigowar Bah ba, sai da ya karaso da sauri ya zauna yana saka hannayensa ya kamata sosai da kula da tarin tausayinta kamar yadda ya saba ya ce" Subahanallah, Anmi YUSUF menene? jikinki ne? ko saboda maganar daurin auren ne Hajia ta fada min yadda kuka yi, bakya tunanin a Daura din ya fi alkhairi maman Yusuf idan ya so sa daidaita kansu?" Kanta ta ɗora a gefen hannunsa idannuwanta a rintse tana tunanin anya maganar nan abar ta yi 'e da shi? duba da wace ta yi jan ragamar zaman watsa ahalinta matarsa ce, A Raunane ta dago tana dubansa, muryarta a tausashe sosai ta ce" Ba'a daura auren bane?" Yana dubanta ya gyada kai a hankali ya ce" Shedu muke jira, Shaheed yace min gayanan zuwa, kuma liman baba ne zai wakilci YUSUF, bakya so a Daura ko?" Mah ta lumshe idannuwanta a hankali ta furta" Ina so, ina so a Daura, idan da hali a Daura shi yanzu yanzu, kuma a sanar a lasifika, ka bani wayarka ka samo min YUSUF din, Ni zan sanar masa sannan in bashi umarnin ƙafarsa kafarta, ka ji?" Da mamaki yake kallonta, sai dai bai yi mata gardama ba, ya dauka cewa adu'ar da aya yi ta yi kwana biyun nan ne Allah ya amsa, dan haka ya shiga neman Layin YUSUF, sai dai bata shiga, aka sheda masa yana waya, ya dan jima ya sake bugawa wannan karron aka ki dagawa, ya rasa dalilin da ya sa ba'a daga din ba, dan ya buga ya kai sau hudu ama ba'a amsa ba , a dole ya mike bayan ya daukowa Mah maganinta ta sha yace ta je dakinta ta kwonta ta nuna a'a bata jin barci akoy abinda take jira, shi kam a dole ya fice dan ana ta nemansa a waya a masallacin Masarautar Bayan fitarsa Mah ta samu ta daidaita kanta, ta je ta dauro alwallah ta zo ta ajiye salayarta ta maida gabanta gabas ta yi raka'a biyu sannan ta zauna rike da carbinta tana ja idannuwanta lumshe, dan tunda ta nemi kadaicewa din ta nuna bata son damu daga kowa sai ya zama ko yan aiki dake lekowa jifa jifa sunna karra kimtsa waje da karra turaran wuta basu shigo ba, hakan ya sa ta samu nutsuwar da take da Muradi ta ringa yiwa Allah kirari, tana ta karra neman kusanci da ubangijinta, ba ji ba gani tana karra yiwa Annabi salati , shauki da nutsuwa na ratsa ta kunnayenta n sauraron babar lasifikar Fada, lalo lalo har ta fara tsinkayo ana gayatar duk wani namijin dake iya halartar daurin aure yanzu yanzu.....hakan ya sa daurin auren ya ringa dan jan lokaci , ama a inda take bata motsa din ba, dan bata tunanin tana iya motsawa in ba kunnayenta suka jiyo mata abinda take son ji ba ...................................................... A lokacin da motarsa ke yin cikin Damagaran ya dauki hanyar gidan Bara'atu kamar yadda direban ya sanar masa ga inda suke, a lokacin ne Shaheed da yan rakiyarsa suka je taron daurin auren sa ba tare da ya sani ba Zuciyarsa yana iya rantsewa ta kumbura a irin yannayin nan da yake ciki, gumin da bai daina ba kuwa ya tabatar masa gudun jinninsa ya jima da wuce ka'ida, idannuwansa kuwa yana iya rantsewa hudu hudu suke gani bama bibiyu ba 'Shin me yasa ake tayata kaucewa umarninsa?, me yasa mahaifiya a gare shi ta kasa taya shi daidaita kansa ya zama cikakken da ake so ya zama?' Wannan sunne tambayoyin da yake yiwa kansa a zaune cikin mota, a harabar gidan Atu, domin yana isowa ya yiwa abokinsa texte cewar yana kofar gidansa, shi kuwa ya yi kiran mai gadi yace ya bude masa gayanan zuwa yana gidan dayar matar tasa ne ba nisa, hakan ya sa ya shigar da motar ya samu waje karkashin wata innuwa ya parker motar ya salami direbanta da tsoro da mamakin ganninsa da kansa yana tuka kansa kuma a nan kuma ga dukkan alamu Hajia da ya tuko ya zo nema? shi dai bashi da halin yin wata tambaya a dole ya juya din ya bar gidan ba tare da ya yi mata salamar cewa an ce ya tafi ba A cikin falon Atu, zaune suke a tsakiyar falon sun baje, RAUDA ta cire lesh dinta tunda ta zo Atu ta bata wando irin mai lafewa a jikin nan da riga katuwa sosai budadiya ta saka ko dan kwali bata saka ba ta yi masu danwake a kicin din Atun sun baje sun zabga masa yaji sunna ci sunna ihu da fira da dariya irin ta aminan da suke aminan junna din nan na kud da kud, dan Atun ta tabatar mata mijinta yau yana gidan uwar gidanta shi yasa ko hijab basu dauko kusa ba Atu na dubanta a lokacin da ta gama shan ruwan sanyi da kyar yaji ya bar harshenta tana haki ta yi yar dariya ta ce" Ina son tambayarki wani abu Ni kam, wai yaya usulin mesg din ku da MALEEK?" RAUDA ta saka birki a kokarin sake kai dan waken nan bakinta, sai kuma ta tabe baki ta ce" Dama bakina da naki nace maki Shi ya min message?" Atu ta dan zarro ido tana kallonta ta ce" Kar ki raina min wayo mana, Ni dan Allah gaya min, dan matar nan tasa tsaf na nemo wace ita, dan a ranar da kika so sakawa ya zane mu ta bani mamaki, ke kin san kirarin da ake yiwa uwarta kuwa? baiwar Allah kishiyar Mamanta tunda aka auro uwarta ta zama kamar hoto a cikin gidan, ke su fa harda tsafi kina ji suke yi, kuma duk daraja irin ta babanta kina ji mamansa surfe take yi a garin nan, dan gaba daya ya manta da tana raye fa, ke Ni sai da na tsorata da na ji wannan abin nace Allah , Allah ga MALEEK ya rab ga Mah, kuma ga RAUDANA, Allah ka sa su fi karfin mugu ya Allah!" RAUDA ta tabe baki tana kallon ta ta ce" Ba zaki gane bane, ki daina hada sunnana da shi da matarsa, dan Ni bana iya cin sauran tuwo!, kuma kina maganar tsafi sai dai lamari na Ubangiji idan har ya kadarto hakan wa Mah dina, bayan wannan Ni so nake na zane yarinyar nan walahi, haka kawai nake tashi da muradin in zaneta, na dai yiwa kaina alkawarin ba Ni ba su ne, da ba wannan ba yarinyar nan so nake in dauraye mata jiki ta yadda man nan da ya gama jika mata fata ya sa ta zama kala biyu, wajen man da kuma wajen bulalar ke dai kamar bayan kado dai ya dace fatar ta zama ko?" Atu ta zarro ido cike da mamaki zata yi magana RAUDA dake kallon wajen kofa a rikice ta duke tana hade jikinta da dan karfi ta furta" Innalilahi, aminin aminiyata kar ka shigo dan Allah!" Ja ya yi ya tsaya ya juya bayansa gaba daya, hakan ya sa Atu mikewa da gudu ta shige ta dauko mata zumbulelen hijab ta dawo ta miko mata ta zurma tana fadin" Aban karima dama kana dawowa warhaka ban sani ba har muka baje? bismillah kai ɗaya ke tafe" Juyowa ya yi yana murmushi, idannuwansa ya dan sauke kan RAUDA, sai kuma ya dauke zuciyarsa cike da matsanancin mamakin abinda ya tarar yau a wajen MALEEK a tausashe ya ce" Eh Ni daya ne aminiyar, aminiyar aminiyata shine kika so ki kawo ziyarar ki gudu Ni ba'a yi zumuncin da ni ba ko?, to tashi ki je Mah ta turo sako wai, zaki ga motar cen wajen shukokin cen na mangwaro a parker " Jin an ce Mah ya saka ta mike da sauri, ko wayarta bata dauka ba ta nufi wajen tana fadin" Sako? ko wani aiken Mah gareta ? ama bata yi kirana ba, ina zuwa Atu" Daga haka ta fita Sai da ta tsaya ta dan dafe kugu kadan tana duduba filin gidan, hakan ya sa ake gannin wandon dake kasa karara sannan ta gano motar ta nufeta a ranta tana ayana' Kai motoci sai a gidan Mah, duk wayewarka sai ka bi watan da kallo alkur'an ' Gannin ba'a bude aka kawo mata sakon kamar yadda aka saba idan wani abin ne ya sakata tunanin ko ba kowa a motar? hakan ya sa a nutse ta karasa ta saka hannayenta wajen madubin dan ta ga ko zata iya gannin ciki, duba da motar a lulube take da bakin madubin nan Har ga Allah kukan kwakwa din gidan suka hannata jin an bude barin zaman direban har an zagayo inda take, sai da ta ji an kama damtsen hannunta an juyota, ta zabura tana ruko ido ta daga dubanta ta sauke a kan fuskar da ta sa gabanta yankewa ya yi matsanancin dokawa a firgice ta gaza wani motsi sai jinta ta yi wannan karron ma an zaunar da ita cikin motar nan sannan aka rufo ta gaza wani motsi sai hannunta da ta dan dago a firgice tana juyawa tana binsa da kallo har ya bude motar ya shiga ya rufo da karfin da ya saka cikinta murdawa zuuuuuu, ta rintse ido da karfi ta jimke hijab din na jikinta saboda irin yadda ya warci motar sannan ga shiga adu'a a cikin zuciyarta har ta bude ido ta ga inda ya nufa ya dauki babbar hanyar Tsatsunburum ne dan haka ta ringa daidaita hakinta har ta dan samu kwarin gwuiwa a hankali ta ringa kallon yannayinsa zuciyarta na dokawa da tarin tsoron yannayin, kasa kasa sosai ta furta" Yayanmu, lafiya dai ko?" Idan har ya tankata to kuwa motar nan ta tankata, gaba daya sai tsoro ya sake lulube ta, ta yi tsuru tana murzar hannayenta kirjinta na dokawa, baban tashin hankalinta ko waya bata dauko ba bale ta sanarwa Mah inda take, ya Allah, kar dai wannan mutumen ya ilata ta? to wai mema ta masa ne fisabililahi? me ta yi masa ne? A lokacin da suka karaso Tsatsunburum yama ta yi sosai, a haka ya tunkari hanyar fada, sai dai sunna daf da karasawa ta ga ya dauki wata hanyar, hakan ya sa ta sake tsorata tana ta kallonsa, sai ta ga an bude wani makeken get da yake da irin kwaliyar get din fadar Idannuwanta tamkar zasu fado wajen kallon dogaran dake wajen da sojawa Bama polisai ba Tana kallon nan suka karaso Cikin gidan, wanda ya nuna mata ginnin kamar na part dinsa, sai dai ai kamar ba cikin fadar ba kasancewar duk sun dauki yannayin jiran ya fito dan su miko gaisuwarsu ya saka shi dakatawa ya dan sauke madubin motar kadan Da sauri Taj ya karaso ya sauke ƙafarsa daya a kasa daya a duke hannunsa a jimke ya furta" Barka da warhaka ubangidana" A cen ciki muryarsa ya furta" Su koma bakin aikin su" Da sauri Taj ya mike ya koma wajen da suke ya sanar masu, sannan shima ya ja ya tsaya ya raba kaffafuwansa ya ba motar baya Idannuwansa dake lumshe ya bude a hankali ya sauke a kanta, a lokacin ta gama marairaicewa ta matso kwallah mai zafi irin ta sa ya ji tausayin nan nata tana kallonsa a hankali ta sada kai ta ce" Yayanmu, dan Allah idan na maka wani laifin a rashin sani ka yafe min, walahi a sanina ba zan bata maka ba, ka yi hakuri ka maidani wajen Mah dina, in sha Allahu ba dai Ni na kuma bata maka ba ka ji?" ta karashe tana matsar kwalar harda dagowa dan ya gani Jajayen idannuwansa a kanta tunda ta fara maganar har ta dakatar, A hankali ya ce" Bani wayarki" RAUDA ta dago da sauri, sai kuma ta sake maida kan kasa, kasa kasa ta ce" Tana gidan Atu walahi ma kuwa" "ina da ina kika je?" Ya sake katseta, yana fitar da huci daga zuciyarsa RAUDA ta dago ta zubawa fuskarsa ido, a hankali ta sake raunana idannuwanta ta yi raurau ta ce" Yayanmu" "ki ce YUSUF din ki Please, yaushe kika fara boye sunnana?" Ya fada yana sake dauke kansa A raunane ta dan duko kadan a cikin motar tana kallonsa ta ce" Na rantse da Allah na san ai kai yayanmu ne, kuma duk abina ai ba zan kama sunnanka ba, dan Allah ka yafewa abinda na maka a baya , idan na kuma ka batar da Ni gaba dayama kowa ya huta ka ji?" Kai ya girgiza kawai ya bude motar ya fita a rikice ta bi bayansa da kallo, da sauri ta bude ta fito ta karasa wajen Taj tana tattare hijab dinta tana waige waige dan samun wajen da kafarta ke iya bata dama,, ta ce" Taj, dan Allah ina ne nan? ko polise station ne? to me na yi da za'a rufe Ni, dan Allah ka je ka sanarwa Mah gani a hannunsa ka ji Taj?' Kai Taj ya sake sadawa, dan shi ba bagwari bane , koda ubangidansa bai sanar masa ga abinda baya so a kalla ba ya gane tunda ya kori maza ya kaucewa ganninta yana fadin" Ki bi shi, fada ce fa, kuma part dinsa ne na baya, idan kika shiga ta nan zaki je falonsa baba Ya fada ne yana sake waje dan ya kula idan ba amsa ya bata ba walahi ba zata tafi ba Tana jin hakan sai da ta sauke ajiyar zuciya ta tatare hijab din sosai kunnayenta na jiyo mata Muryar mai lasifika yana fadin a zazauna yanzu za'a daura aure, a zazauna yanzu za'a shaida daraja a kan mai daraja, kowa ya yi shiru a saurari bayani sosai ta yi mamakin sabon salo, koda yake a aurensu an sanar a lasifika ama ba irin haka ba, kawai an sanar cewa an daura auren ne dan kowa ya ji, ama wannan ko auren waye oho sosai ta ci damara da hijab din nan ta bi bayansa Tunda ta tunkaro ta ringa jin Muryar mata, ana miko gaisuwa da girmamawa, sai kuma ta ji Muryar AMNAH da alamun murmushi tana fadin" Ashe kana nan Sir, su Mama ne suka zo gaishe da su Mah, shine suka leko mu gaisa" Ta so ta juya, sai dai ta san ko ta juya din ba za'a barta ta fita ta cen ba, sai kawai ta rintse ido ta karaso tana son kunce hijab dinta ta kasa sakamon abinda amsa Kuwar lasifikar Masalaci baba ke fadi tana karawa a lokacin da du mamakin ganninta da inda ta fito ya saka su AMNAH zuba mata ido , sai kuma abin nan dai da kamar idan ka ji da farko baka ji da kyau sai da kowa ya yi tsai har kamar a hanna junna sauke numfashi saboda a ji da kyau , dan kamar amsa Kuwar nan, ko shi mai amsa Kuwar sun haukace ko ace da su rikakun yan Allah tsine da suke fadin abin nan ne? to dai sanarwa ta iso da magana kamar haka " *ALHAMDULILAH, ALHAMDULILAH, ALHAMDULILAH, A GIDAN MUTUN MUKE GABAN SARAKAI MUKE, DA IYAYENMU MUNA SANAR DA DUKAN WANDA YA KWANA YA TASHI DAURIN AUREB MALEEK DIN MU, UBAN GIDANMU , A KARRO NA BIYU MUN SHAIDA DAURIN AUREN MALEEK YUSUF BELLO DAN BELLO DA RAUDA MUHAMADU A BISA SADAKI JAKA HAMSIN CEFA JAMA'A KU SHAFA FATIHA....FATIHA AMEN LIMAN*" 😭😭😭😭😭wakihu Ni kam tsoron rigimar nan nake, jama'a ku kwato yar Mah, gata da wando tsigi tsila, gata daga ita sai ranta a nan din kau???? a dai ringa yi ana amsar BONANZA 😭😍😍😍😍😍😍😍😍😍 ta LITATAFAINA SU 22 CIF a farashi mai RAHUSA 1k in sha Allah, a TUNTUBENI a saman numbana kamar haka 93811618 Azl 54 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo AMNAH ce ta fara duban mahaifiyarta a firgice, da sauri ta nufi wajen kofar ta bude gaba daya ta yaye labule tana kasa kunnenta, dan sai take jin kamar bata ji da kyau Ai kam kamar kowa hakan ya so, dan harta shi sai ya yi tsai yana sake shurarawa dan shi dinma sai ya ji kamar baya ji da kyau abinda ake fadin Radau kunnayensu suka tabatar masu abinda suke ji gaskiya ne, hakan ya sa jikin AMNAH kwasar rawa ta juyo tamkar zata kifa a rikice tana kallon mahaifiyarta tana fadin" Mama, mama, kina jin abinda nake ji?" Mahaifiyarta ta mike da sauri dan tareta, domin ba zata so ace ta nuna komai a haka ba, ba zata so ace ta bar abin a yi gaba da ita da baki a yanzu ba, hakan ya sa ta manta tarin abubuwan dake cikin jakarta ta saki jakar, jakar kuwa irin jakunkunnan nan ne masu abin budewar nan irin mabalin nan, gashi an cika mata kaya an kwareta sosai sai kawai ta bare a nan ta zubo da kayan dake ciki, wa'inda suka sauka a idannuwan YUSUF domin har yanzun shi bai wani zabura din nan ba, yana ci gaba da sauraron abin ne kamar dai bai wani yarda ba din nan Da sauri dayar da suke tare wace hijab din ta masa wani irin sakawa ta duka tana kwashewa jikinta na rawa da sauri ta ringa cusawa a jakar sannan ta matse jakar, hakan ya sa YUSUF sake duban kaffafuwanta lokaci daya yana dauke kansa hadi da dantse lebensa na kasa cikin kawar da kai kirjinsa na neman yi masa zafi Da sauri mahaifiyar Amnah ta tareta jikinta tana fadin" Amnah, meye haka, subahanallah meye haka, ki nutsu mana,, ga mijinki zaune ki nutsu mana, menene haka ne wai?" AMNAH ta rukunkume hannayen mahaifiyarta ta fashe da wani irin ihu tana cuje dankwalin kan nata Da Sauri mahaifiyar Tata ta sake riketa tana rufe mata baki ta dan sake risinawa tana fadin" A gafarcemu yalabai bari mu kaita ciki mu rarasheta, ta yiwu abin ne bata sani ba shi yasa ta rikice haka, ama in ba Amnah ba meye a ciki, Allah ya sanyaya Allah ya saka alkhairi" Hannunsa mai dauke da agogo na wajen hancinsa yana kallon mahaifiyar Tata tsai cikin ido har ta gama kisisinarta ta juya da Amnar da karfi , a lokacin ne ya ga sauran biyun sun juya zasu bita Kasa hakura ya yi a nutse ya mike ya fara nufo su , sai dai gannin RAUDA ta nufi hanyar fita ya saka shi dakatawa yana dubanta ya ce" Ina zaki je?" Turus ta tsaya ta juyo ta dube shi, ido cikin ido kanta na sake daukan ciwo da sarawa Da hannayenta ta ringa nuna masa sai kuma ta budi baki kamar bata da Hausa tana fadin" Mah, Mah,, Mah zan je" Idannuwansa ya lumshe da hannunsa ya yi mata alamun ta shiga wani sashe a cikin sashen falon kafadunta ta make ta sake juyawa da sauri sauri gudu gudu Da sauri ya juyo ya bar niyar abinda ya yi ya damkota ya cirata sama, hakan ya sa ta kwala ihu ta shiga kokarin kwace kanta ido rufe tana fadin" Kai, wayo Allahna ku taimakeni, wayo ka saukeni ka saukeni in tafiyata, wayo yau yan masalaci kuma sun haukace ko menene? innalilahi Mah, Mah....." Tana zunduma masa ne yana tafe da ita har ya karasa wajen gadon nan ya dire ta gannin zata kuma tashi ya saka shi saka hannu guda ya mayar da ita ya zarro idannuwansa yana kallonta ya ce" Idan kika tashi ba tare da nace ki tashi ba sai na baki mamaki yau!" A rikice ta yi tsugune tana kallonsa hawayenta na zuba, shi kuwa ya karasa wajen wayar dake jone ya ciro ya saka numbobi ya dana kira jim kaɗan aka daga, a tausashe aka ce" Yanzu ka ga damar kirana ko? ai tun dazu Ni nake kiranka ka ki dagawa, na zata ba zaka nemeni ba isashe!" Kai ya sada yana dan murza goshinsa, a hankali ya furta" Me yake faruwa ne Bah?" Bah ya tabe baki yana cikin ba dama , dan kuwa jama'a sai Allah sanya alkhairi ake yi, ya ce" Ka gane cikin haya haya nake, an kuma tabbatar an isa da kai ne an daura maka aure da Baby, ka kashe kawai idan na ga dama ma idasa tattaunawa " Daga haka Bah ya katse kiran ya ci gaba da shagaalinsa Tsai ya yi da wayar a hannunsa, a hankali ya juyo ya zuba mata ido, sai mutsu mutsutu take yi a saman gadon a tsugune da takalmin ta abinta Ajiyar zuciya ya sauke bayananiya sannan ya saka numbar Taj ya danna kira yana dagawa a hankali ya ce" Cikin bakin iyayen nan na Amnah akoy namiji, mai sanye da farin hijabin nan, idan sun fita ka bi su a boye bakin inda suka rabu da shi ka sake binsa a boye, ina son duk wani informe a kansa, kafin ka dauko min shi ka kai shi baya ka rufe............." Hankali tashe Taj ya amsa yana tunanin abinda zai je ya dawo, innalilahi Wa inna ilaihi raj'une namiji? yau sun shiga uku, Allah ya takaita fushin sir dan walahi sai ya wujijiga masu kwonciyar hankali, innalilahi duk irin yadda suke takatsantsan ashe akoy wanda ya fi su? koda yake tare suka zo da Amnar suka shige kowane da hijab da wahala su iya ganewa Kai Amnar nan walahi sai ya ji ya karra tsanarta, shi baya son mace marar kamun kai a rayuwa, yau kuwa zai ci ubansa namijin nan,dan walahi kafin ya rufe shi sai ya masa salatu ta biyu, ta yiwu bai yanku da kyau bane ya sa yake iskanci! Yana datse kiran nan ya dubeta da dan karfi ya ce" Ke wai meye kike wannan abin?" A rikice RAUDA tana sake matse cinyarta cike da nauyin maganar ta ce" Fififitsari ne nake ji tun a gidan Atu wowowwollah yi zan a nan" Ido ya dan zarro yana kallon a inda tace zata yin Da dan sauri ya karaso yana girgiza kai yanuna mata kasa yace" A'a gaskiya sauko sauko je bayi ki yi" Ya fada yana dubanta Saukowa ta yi tana dubansa sai kuma ta wuce da sauri tana jin kamar zuciyarta zata fito daga kirjinta ta wuce bayin tana rufewa ya dago idannuwansa a hankali ya kai zaune saman gadon yana dan sake bude idannuwansa a hankali ya furta" What?, Really? Yah Rab" Yana rufe bakinsa ta fito sai sake baza hijab din take ya ja ta tsaya a gabansa ta ce" Tafia zan yi wajen mamana!" Shima ya dago ya zuba mata ido wata yar diris abinta sai tarin rashin kunya Ya tabe baki ya ce" Ba inda zaki je, ki bari mutane su ragu mu je nima na ji abinda ake nufi da min auren dole a Yau!" Ido da baki ta saki tana kallonsa, dan yadda ya yi maganar da harde hannayensa sai ta ji eh walahi kamar dai da gasken auren dole aka yi masa Baki ta tabe ta dafe kugu da yannayin tashen fitsara ta ce" Eh kam, nima abinda zai kaini kennan, dan kuwa in dai auren aka yi niyar min a kaini wajen da ya dace, ba wai gidan da matar gidan take mahaukaciya ba!" Ido ya kausasa yana kallonta da gaya ya nunota da yatsarsa guda ya ce" Kin ga, kar ki zagar min matata, kar ki saki ki zagar min matata!" RAUDA wani irin bakin ciki da daci ya tsaye mata a zuciya tana kallonsa ta ce" Ita din banza ita din wofi, bi bata isheni kallo ba Allah la kuwa, kuma sai na zane ta duk inda na hadu da ita, ita nan har ta iya raini ko? zan gwada mata na fita iyawa, banza mai kan munafukai da ita algunguma yar daudun banza da wofi, Ni da ita Allah ya isanama walahi!...." ta karashe tana fashewa da kuka ta nufi darduma ta kabarta sallah tana hawayenta, shi kuwa ya zuba mata ido a ransa yana ayana' Ka shiga uku YUSUF, ka dai ganta nan ko tanada hankalima ko babu? Allah masani, gatanan dai ita kadai ma sai ta shiga fada, kai kuma haka taka kadarar ta kaika ko? Allah kennan, ko sallar ta meye take yi? ko la'asar ce bata yi ba?' Gaba daya tarin fushin da yake ciki na dazu nema ya yi ya rasa, sai wasu abubuwa da suka same shi suka tsaya masa a rai, ya zuba mata ido kawai yana kallo a zaunen nan "AMNAH!, baki da hankali ne? ki nutsu nace maki yar iskar banza da wofi kai!"Mahaifiyarta ke fada da karfi, bayan sun hadu sun ririketa ta kubce masu ta ringa watso kwalaben turarukan wuta da na ruwan dake jere masu tarin kudi, ta gama ta ringa fasa kayan saman sif duk abinda ta hadu da shi sai ya rotsa tana ihu tamkar sabuwar kamu A haukace tana ihu da kuka ta ce" Aure?, mijin nawa aka yiwa aure? Kishiya aka min ko tarewa ban yi ba da mijina?,Ni Amnah aka yiwa kishiya? kishiyar ma wannan yar matsiyatan da suka mutu basu da ko tufafin kansu masu kyau?, Lalle nice ajalin yarinyar nan, kuma ko uban waye ya aurawa mijina wata sai na zame masa balaki da masifa a duniya, walahi sai na zame masa Azal din da zai gwamaci mutuwa da rayuwa, wayo Allahna sun kashe Ni sun kashe min kuruciyata!......." ita ihu ta iya yi, Bata san mahaifiyarta ta fi ta Shiga mummunan yannayi sakamakon wannan abin da suka tardo Basu taba hasashen ko nan da shekara goma an nemi yiwa Amnah wannan cin zarafin ba domin sun yarda da isar y'arsu dari bisa dari....shin me Amnah ta rasa? in me ake so idan aka zo kanta za'a samu, yanzu ace ita ce aka yiwa y'arta kishiya? y'ar da ta kawo shekaran jiyan nan? y'ar da ko fuskar mijin bata gani ba? yau ko ita uwar wane kakar wane ta fi karfin kishiya bale Amnah sabon jini?, Amnah yarinyar da samari suka ringa wawa ama suka ki basu dan sai ta zaba ta darje, gashi yau sun shigo da abinda suka yi niyar fara binewa a yau din sai gashi ya shigo gidan a lokacin da basu shiryawa ganninsa ba?, sunna cikin kokarin ganin ya shige nasa dakin wannan abin ya faru? da ace Amnah zata yi shiru ta bincika zuciyar mahaifiyarta da sai ta tsorata da abinda zata gani wanda ya dame nata ya shanye "Hajia ya dace a tausashi Hajiar Tsatsunburum, ta kwontar da hankalinta auren nan a yau in ya kwana shege nake ba dan halal ba, meye na daga hankali mu da muke da masu bugun kasa a hannayenmu, sunne karyar mu, sunne gatan mu, dan Allah ta yi hakuri kar ta yiwa kanta rauni mu tsaya jinya mu kasa magance matsalar nan" Dan daudun ya fada yana sake riƙe hijabinsa a jikinsa da kyau dan gudun kar a shigo a ganshi ba hijabin, ama a dazu ya tsorata fiye da tunanin bawa, kai, bai taba Sannin ana rawar haba ba sai dazu da ta zubar da abubuwan nan, yau da an kama da ina zasu saka kansu? shegen Tsatsunburum ya fi shegen kowani gari iya iskanci, ya tabata a dame an dame shi, shima shegen kwadayinsa ne da sai ya kai ya baro shi! "Ai wannan ka barta kawai, ku ku tafi kawai Ni kam sai na ga ta nutsu kar aje in bada baya ta halaka kanta ko ta tarda su ta yi wata barnar da za'a kasa gyarawa, bata ganewa ne Ni bayan ubanta ya aureki na haife su ai ya taba gwadawa, karshema ya zama in dai ba da Ni ba baya iya anfanar kowace mace, ita ba zata bi abubuwa a hankali ba sai ta dagawa mutane hankali a kan banza, yarinyar cen kuwa da kike gani duk inda ta fito dama akoy wata a kasa tsakaninta da shi dan ban san ubanda take nema a wajen da kika ce wajen sirrinsa ne da damamen Wando ba, na jima da ce maki ki yi kokari ki bashi abinda yan waje suka sabar masa ama kamar ba mace ba kina dari dari, idan ita ke bashi ai shikenan ko me zaki mata ta shawo da ke! shashasha Amnah ban san idan ina fada maki abu inda kike sauraro ba, ki yi min shiru da ihun nan na jijika maki Wadinnan bita zaizai din ki yi duka yadda akace ki yi na kuma dafa maki na dafawar ki ci, ki kashe wayar ki saboda yan tsegumi ki barta sai mun fitar da yarinyar kya kunna, ka ga Habu ku je kawai dan a yi tunanin nima na tafi ku je ta yiwu in kwana a nan" Dayar abokiyar tafiyar kam kasa cewa komai ta yi, dama ita din bakuwa ce a duniyar sharafin nasu, sai take kallon su a bakin sani cike da tunanin anya kuwa igiyar nan da ta riga mai kwari ce? domin ga shiga jikin Hajiar ne dan ya samu itama ta gagari zama da kishiya, sai ga wani abu da ya wanzu mai rikitar da kwakwaluwa ita abinda ya fi bata mamaki shine ire iren zantukan da bokayan nasu suka ringa yi masu yanzu yanzu , wajen boka biyar suka je, kowane ya yi tsubace tsubacensa aka zuba masa kudi ya bada maganinsa da bayanin abinda za'a yi da shi a binciken bokayan basu ga maganar kishiyar bane bayan ana nufin su din sun san gaibu? (Astagfrullah), To kennan su dinma makafin ne ta yiwu fiye da sauran al'umma? kuma a furucin Hajiyar ta sake shiga a cikin tunani, da gannin tabas ta riki rubabiyar igiya, domin abin kamar na mahaukata? Shin a me ta dauki gidan sarauta ne? duk inda take tunani sun shalaketa, walahi in me take tunani sun fi ta, sai dai a daidaita zama a dubi junna dan a zauna lafiya, ama ita nan har mai nema ce?......., mutumen dake zaune a gidan sarauta kansa sai ya baka abubuwan tsari masu yawa bale SARAKAI!, kofa yake shi tsafi ai kuma gaskiyar mai shi, ama ita tana tsoron irin yadda ake nuna har yanzu Amnah ta gaza zama cikakkiyar mace mai yanci da takama da aure irin na kowa ya saka take tunanin anya ba hanyan biri ne ake yi a tsakanin junna ba? ....Uhum, ta yiwu wanda suke dako ya jima da gannin makwoncinsu, dan haka ta mike da sauri tana karfafa masu gwuiwa ta fara ficewa dan ba zata so wata fitina ta haɗa su da YUSUF ba, duk wanda ya san shi a da, zai kiyaye shi a yanzu! Tunda ya tafi sallah RAUDA ta sake kuntata zuciyarta da tunanin eh lalle auren nan ba dai ita RAUDA ba To mana ai kowama zai ce ba dai RAUDA ba, Yaushema ta rasa miji harda wani zai kuma amsa sunnan mijinta? burinta ta koma makaranta ta fara sana'a mai kwarin gaske, shikenan. Sai a ce haka?, me kennan? ya sameta a bagas walahi in dai a haka ta zama matarsa to tabas ta gama zubewa har kas Idannuwanta ta rintse tana sake daukan damarar yaki da shi, dan YUSUF ba shine mijin da take mafarki ba, ita ai Bama ta son mai mace, kuma bata son namiji mai takama! Mikewa ta yi tana kabe jikinta kamar wace ta yi dati ta juya ta bude kofar a hankali ta fice ta nufi hanyar baya dan in dai Allah ya taimaketa a bude ta nan ne kawai zata iya guduwa ba tare da an hannata fita ba, dan ta sani in dai ta wajen babbar kofar falonsa ne babu inda zata je ba tare da izninsa ba Da sauri ta kama kofar part din Mah ta bude ta shige har tana waiwaye ta sauke ajiyar zuciya da sauri ya nufi dakin Mah ta tura ta shige ta maida kofar ta rufe tana sake sauke ajiyar zuciya ta juyo da nufin yin salama idannuwanta suka shiga cikin na Mah , hakan ya sa ta......... Happy juma'a yan uwa Ta juyo da nufin yin salama idannuwanta suka shige cikin na Mah, Hakan ya sa ta ja da sauri ta tsaya tana kallon Mah din ta kasa yin salamar Mah ta bita da kallo daga sama har kasa, yannayinta ya ganar da ita ta ji abinda ya faru, dan haka ta dauke dubanta a kanta ta idasa zama saman kujerar falon tana fadin" Inaga a fitar baby an koya mata rashin salama!" Da sauri ta kai hannunta tana shafa fuskarta, sai kuma ta karaso tana cire takalmin kafarta ta haye saman kafet din tana dan murzar hannayenta muryarta a rarrabe ta furta" Mah, ina ina yini, ina gajiya" Mah ta sake dagowa ta biya da kallo tun daga sama har kasa, a tausashe ta furta" Lafiya alhamdulilah, ina kika baro tufafin ki?, wannan din na waye? a ina kika saka? kuma waye ya kawo ki?" RAUDA ta ringa raraba ido, a hankali ta ce" A gidan Atu ne da na je na cenza, kayanta ne dan zan yi girki, to kuma muna fira yace ace kin aiko wani , shine na zo ban san shine ba, sai kawai ya kawo Ni nan din" Mah ta sake tsare fuskarta da kallo ta ce" waye yace din?" RAUDA ta sada kanta, a hankali ta dago tana kallon Mah ta ce" shi Yayanmu" Mah ta gyada kai, sai kuma ta yi dan murmushi ta ce" Ok, je ki yi wanka ki cire tufafin nan ki same Ni a dakina" RAUDA ta gyada kan itama har ta juya Mah ta ce" Baby?" Da sauri ta juyo gabanta na dan faduwa Mah ta ce" Me zaki ci in dafa maki?" RAUDA ta sada kanta tana jin wani irin zabi na sake ratsa mata jikinta dangane da Mah A raunane ta ce" Komaima zan ci Mah" Mah ta gyada kanta ta sake mata alamun ta je Tana tafiya Mah ta mike ta nufi bangaren Hajia Ta sameta zaune tare da Nana da y'ar gidan Nanar sunna maganar da kana gani zaka gane ba ta dadi bace Ba tare da ta nuna wani abin ba ta gaisar da Hajia, sannan ta juya dan komawa Kamar daga sama ta ji Nana na gaisheta, kafin ta rufe baki y'arta ta gaisheta itama Dakatawa ta yi ta juyo tana kallon su, kamar wace ke son gane in su din mutane ne ko ba mutane ba a zaune, sai kuma ta dan dauke dubanta ta wuce dan har ga Allah bata yarda cewa ita ake gaisarwa ba, ko kadan A raunane Nana ta kalli Hajia ta ce" Hajia , kin gani walahi Ameerah ce bata son zumunci da Ni, Ni a yanzu bani da abin fada sai dai na ba kowa hakuri, ama dan Allah ki saka baki a cikin lamarin nan , ki duba ki ga yarinyar nan a halin da take ciki, Hajia walahi Bama barci, ance aljannu ke damunta , ance jifa ne, Hajia ga lamarin YUSUF da ta kakabawa zuciyarta, Hajia itama fa jikar ki ce, kuma tana daya daga cikin jikokin ki mafi soyuwa a zuciyar ki, ama sai ki kyaleta ta shiga wani hali a kan abin da kin sani sarai kin fi karfinsa a wajen iyayen YUSUF? shi kuwa idan mahaifiyarsa tace ya yi abu ko meye yi yake yi Hajia, ya'ya za'a yi ace an karra daura masa wani auren tana raye ba da ita ba, dan Allah Hajia ki ceci jikar ki" Hajia ta sake duban DAYANA, wace ke zaune gaba daya kamar ba ita ba, Dayana ta bushe kau, sai bakin baki da kwala kwalan idannuwa, kana kallonta ka ga zaburariya, Kai ta girgiza tana kallonta ta yi murmushi ta ce" kin ga, Ni ba zan yi masa wani auren hadin ba kuma, wanda na yi masa ya isa, a gabanan idan yana da damar karra wata sai dai zabinsa, idan har ya yi niyya ya daidaita kansa da ita ba zan hanna ba, in kuma ya ki , ki yi hakuri,......da ace zaki ji shawarata da na baki Nana, kin ga Dayana fa a yanzu ba wai maganar aure ne ya dace a yi mata ba, ya dace ta je ta ga likita tun daga kan na lafiyar jiki, na ƙwaƙwalwa, da na harkar shaye shayen nan, idan Allah ya sa ciwonta bai yi nisa ba sai ki ga ta zama mutun ta yiwu idan ta dawo hayacinta ki ga Bama zata so shi ba, ama a yanzu fisabililahi ko ke aka ce a ba RISLAN irin haka ai kya ce a'a bale YUSUF fa sarki ne, Allah ya sanyaya ko menene ama a ringa yi ana yin abinda hankali zai dauka, Ni nan da kike gani wai ki ce na kasa yafe maki ko me? haba yaushe zan tsaya ci gaba da rike ki a rai bayan Ni na haife ki? ai da kin jima da watsewa, a kulun idan na yi sallah sai na kama sunnayen ku gaba daya da na haifa da wa'inda na rike na rokar maku gafara da shiriya da kariya da kyakkyawan karshe da sakamakon aljanna, ba zan ware ki ba saboda butulcin ki, sai dai zan yi takatsantsan dan kuwa Nana walahi ban yarda da ke ba, ina sakawa raina kina iya cutar da Ni mahaifiyar ki, tunda kika kwashe lokaci mai tsayi kina cutar da d'an zumun ki, ku je kawai Allah ya sanyaya" Wadinnan kalamai na Hajia sun karra rikita duniyar Nana, takan ji a duniya ta fi kowa asara a da dan ta zamto mace wace ba zata yi mulki ba kuma ƴaƴanta ba zasu yi mulki ba, sai dai a kwanakin nan da take fuskantar tsantsan tashin hankalin duniya daga kowa ya sa ta fara manta abinda ya jaza mata bakin jinnin ta dawo ta ringa fuskantar rayuwa da abinda ake kira shiga ukun duniya da lahira, domin ko mahaifiyar da ta kawo ta duniya basu da wata hulda ta kusancin da ta wuce hangen nesa da kiyayewa gudun kar ta cutar da ita Tana gaba, Dayana na biye da ita kamar zata fadi suka fito suka nufi bangaren su sunna shiga Dayana murya a bude kamar yadda shaye shaye ya bude mata ita ta dubi mahaifiyarta ta ce" Mama, yanzu yaya zan yi kennan?" Murya na rawa, tana daf da fashewa da kuka ta ce"Hakuri zaki yi, nace hakuri zaki yi kamar yadda kowa ke yi idan ya rasa wani abin, ki yi hakuri da shi, ki yi hakuri nace Dayana!" Dayana ta sake kallonta kirjinta na dokawa ta ce" Mama, idan ban same shi ba, ina iya mutuwa" Nana ta kafeta da ido, ido cikin ido ta ce" Sai ki maida hankali!" Daga nan ta barta nan tsaye ta nufi dakinta ta fada saman gado ta fashe da matsanancin kukan da ta kasa hanna fitowar amon sa, kuka mai gunji da tashin hankali..... TABAS maganar YUSUF ta tabata a lokacin da yace da ita sai ya adabeta, gashi kuwa yana adabar Tata da muguwar adabar da ko kallo bata ishe shi ba, yana kona duniyarta da shiru da kyautatawa, bai fito ya yi fito na fito da ita ko wata fitinar ba, ama a haka ita ke wahala fiye da kowa a rayuwar nan ta yanzu, ita ta san an gama gamawa da ita, ba ɗan uwanta, ba mahaifiyarta ba mutanen gida da na waje sai daidaikun dake karra tunzurata zuwa karra tsanar YUSUF din, su dinma tana iya rantsewa ingiza wawa suke yi mata .......wannan kennan..... Bayan fitar su Nana da kusan minti ashirin ya shigo falon Hajia gannin bata falo ya karasa dakinta yana salama, kana ganninsa zaka gane yana dauke da magana ne wace ba zai bari ta kwana ba Hajia dake kwonce saman gadonta ta kama ta zauna tana kallonsa ta ce" MALEEK ne ? Barka da warhaka ina fatan lafiya kake?" Baki ya fara cunowa, kafin ya jingina da bango yana kallonta ya ce" Shikenan Ni kennan sai a ringa yi min auren dole kina kallo ba zaki hanna ba?" Hajia ta kafe shi da ido, a hankali ta ce " Auren dole kuma?" YUSUF ya gyada kai tana kallonta ya ce" TABAS!" Hajia ta dauko hannunta ta dage habarta ta ce" Da RAUDA din aka yi maka auren dole MALIK?" YUSUF ya kuma gyada mata kai ya ce" Gaskiya ya isheki hakanan, kin ga daga wannan a barni na zaba, dama shi na shigo in fada maki!" Har ga Allah Hajia sai ta rasa amsar bashi, ya zamo ta rakashi da ido har ya bar dakin nata ya rufo mata ya tafi sannan ta sauke ajiyar zuciya tana girgiza kai, sai kuma ta saki murmushi ta yi addu'a ta sake komawa ta kwonta dan sarai zata nuna masa auren dole, ba dai auren yace ba ko? hum! " Baki ji ana fadin karfe duka karfe bane? yi a hankali kar ki jimu, ki kuma cinye sumul ki zo nan ki kwonta!" Mah ke fadawa RAUDA dake kokowa da allura zaune gaban plate din abinci Dagowa ta yi ta kalli wajen da Mah ke nufin ta kwonta, saman gadonta, sai ta dan yi shiru tana tunanin rabonta da kwana saman gadon an dan jima fa, kuma ita ta so su yi magana da Mah ama gaba daya Mah ta ki bata dama, bata san dalili ba ajiyar zuciya ta sauke ta shiga cin abincin tana tunani a cikin ranta, ita kadai sai ta jinjina kai ta kuma girgiza ta dantse lebe ta kuma dauke kanta har ta gama ta kwashe kwanukan ta kai kicin ta darwaye ta dawo da sauri ta shige dakin Mah dan bata so su hadu da Salima a yau, bata san yaya zata iya da tambayoyin Salimar ba, bata san ko tana da amsar ba Salimar ba, dan ita dinma bata da amsar ba kanta da dan gudu ta shige ciki ta karasa ta yi brush ta fito ta kwonta ta jima tana juye juye kafin ta yi barci, duka Mah na zaune tana kallonta har sai da barcin ya dauketa sannan ta yi murmushi ita kuma ta mike ta haye salaya ta shiga nafila da Adu'o'in tsari wa ƴaƴanta da fatan Allah ya saka albarka a wannan hadin ya kuma kawo sauki a duk wata fitina dake tafe da hadin....... ____________________________________ Har kusan karfe goma sha daya na dare ya nufi bayan gida, wato wajen sirrin da kuma wajen da suke buyan yan jagaliyansu Taj dake tsaye kikam ne ya yi gaggawar dukar da ƙafarsa kamar yadda ya saba sannan ya mike bayan ya bashi dama zama yayi saman kujera yana duban Taj, hakan ya sa Taj din zaunawa yana fuskantarsa a tausashe ya ce" Dangane da ISHAK hakane, aiki aka bashi, kuma yana da vidios da yawa da hotuna da voice note wa'inda na yi mamakin dalilin da yasa bai ba mutanen da suka saka shi aikin ba har aka yi nadin sarauta, kuma duk irin yadda ka ture shi a jikinka dan ka ga iya gudun ruwansa bai falasa ba, ama Ni dai na gaza hakuri sai da na bugar da shi sosai na kwaso komai, gasunnan kai nake jira na kona su " YUSUF ya yi murmushi yana kallon Taj ya ce" Ya cenza nufinsa a kaina ne, shi yasa ya kasa yada abubuwan da ya dauka, zan karra bashi wata jarabawar idan ya cinye zan yafe masa, dan rayuwa ba zai yiwu mutun yace shi da kowa yana rikici ba, kuma idan kace zaka kasance mai riko wata rana ko da kanka ba zaka yarda ba, Allah shi kyauta " Taj ya amsa da amen sannan ya dora da fadin" Mutanen nan su biyu ne kawai suka fito da sir, dan daudun nan da dayar matar, mahaifiyar Madame na ciki, na kamo dan daudun har yanzu barci yake yi dan na masa allura ne," YUSUF ya kalle shi da dan yannayin mamaki ya ce" Are You sure tana ciki?" Taj ya tabbatar masa hakan ya sa ya yi murmushi ya mike yana fadin" Dan firgita shi dan ina so daga an tambaye shi ya kai ku wajen bokayen matar Please" Murmushi shima Taj ya yi yana shafa sabuwar askar da ya siyo, shi fa sai ya yi masa yanka dan ubansa dan ya gani meye damuwar da ta saka shi saka hijab? Tunda ya shigo falon kaurin abubuwan da suka turara ke yi masa maraba, dukda an sa turaran wuta akoy kaurin abin Dakinsa ya wuce direct ya shige bayi ya bude wata loka ya ciro hade haden wajen Bah ya haɗa ya yi wanka, ya dauro alwallah ya fito ya haye salaya A kalla ya kai karfe biyu na dare ya sauka daga saman salayar ya nufi dakin nata hankali kwonce ya je ya kama abin budewa ya bude sannan ya kai hannunsa wajen kunna fitila ya kunna, hakan ya sa dakin ya garwaye da haske a lokacin da mahaifiyar Amnah ke kokarin sake hada wani garwashin da boka yace su yi tsakiyar dare su turara a kowani sako da lungun baban falon gidan hakan zai sa ya shaki warin koda baya so, idan har ya shaka an gama shi zai nemeta da kansa ko a gaban waye A tsorace ta saki kaskon a lokacin da ta juyo da sauri gannin haske ya gama dakin Shima sai ya yi alamun ya ji mamakin ganninta din nan ya dan juya yana fadin " shima sai ya yi alamun ya yi mamakin ganninta a irin wannan lokacin, dan haka ya juya da dan saurin magana ya furta" ya Salam, i'm sorry" Sai kuma ya fice da sauri yana rufo masu kofar Rikicewa ta karshen tashin hankali sun shiga a wannan lokacin daga ita har uwar sai suka manta abinda suka so yi, suka shiga kai kawo da tunanin hanyar fita dan a lokacin mahaifiyar ta nuna zata tafi , da kyar suka gane lokaci ya ja komai balakinsu da isar su basu isa su fita a wannan lokacin daga fada ba, a dole suka nemi waje suka yi tsuru tsuru kwanan zaune , dan jira suke yi kiran sallar asubahi ta samu ta fice a gidan, saima suka kasa gane abinda ya zo nema, karshe uwar ta ringa nuna ai kawai kar su daga hankalin su ta yiwu aikin boka tuni ya ci, ya kawo kansa da kansa ne, sai dai tsoro ya hanna su karasa turare turaren nasu da kuma kasa samun bacin kirki har asubahin ta yi suka ringa dako har aka fara fita Masallaci sannan ta samu ta yi wuffff ta fice a gidan ________________________________ Tunda aka yi sallar asubahi Mah ta zaunar da ita a bakin gado tana fuskantar ta ta shiga labarta mata asalin Wacece ita, wanene Bah a duniyarta a da, abinda ya faru da su, irin fitintinnun da ta ringa gani tun daga yan uwanta har zuwa dangin mijinta da wasu mutanen, har zuwa yanzu ire iren abinda ta gani na cenji wanda ya fi rikita mata lissafi, dan a yanzu ana so a cakula ta, a da tana bambance wanda ke sonta da wanda baya son ta, ama a yanzu du an hade mata tunani bata gane komai ƙarara sai dai ta bi da kallo A hankali ta nisa tana kallon RAUDA dake share yan hawaye lokaci zuwa lokaci tana rike da hannun Mah A tausashe Mah ta ce" kin ga a jiya, na ji tashin hankalin da ya so rikitani, da kyar na iya hawa salaya na fadawa Allah har na samu sassauci , a jiya ne Hajia ta bani umarni a matsayinta Na uwa a wajena kan a hada aurenki ke da YUSUF , ta nuna na isa da ke zan maki magana, na nuna idan kika ki fa? ta nuna na isa da ke, na fito na je part din Hajia dan na amshi wayar Salima na yi kiran ki dan a lokacin tawa a hannun Hajia sai kawai na tarda Amnah da mahaifiyarta da kawayen mahaifiyarta sunna furuci kamar haka..........." Ta kwashe komai ta sanarwa RAUDA wace ta kwalolo ido kirjinta na zafi da jin lalle za'a ci uwar sabada ita da Amnah da uwarta dan walahi talahi furucin da suka yi a kan Mah sai ta rama, dan babu ɗan da aka haifa da jinni da zai zagar mata uwa ta kyale shi, hakan ya sa take dantse lebe tana matse hannu tana adu'ar a gama firar nan ta tarda Amnah su daku idan ya so a rufeta a kurkukun masarautar! Mah ta yi shiru kirjinta na dokawa a hankali ta ce" Sai gani sanadiyar abinda na jiyo da kaina na nemi babanku aka je aka daura maku auren da ta yiwu zaki ji kin tsane Ni, dan na nuna son kai, na nuna karfin ikon kina min biyayya na kakaba Maki auren da ba lalle ki so ba domin kamar yadda kika sani YUSUF baya ji, Yusuf ya yi zaman bin mata, YUSUF mafadaci ne, baya jin magana a da, a yanzu Ban san ko har yanzu yana aiyukan nan mararsa kyau ba ko ya fasa? abu daya na sani ba kowa zai so aurensa ba, komin mulkinsa ,komai kudinsa ba kowa ne zai so kasancewa tare da shi ba, shi yasa na zaunar da ke dan na roke ki......." A hankali Mah ya sada kanta, zuciyarta cike da tsoron amsar RAUDA, dan walahi ba zata so ta ji wani abinda zai rikita mata lissafi a kan hadin nan ba, ta ji ta karra tashi da kaunar hadin a ranta bayan doguwar adu'ar da ta yi a jiya, dan haka a tausashe a kuma raunane ta ce" Dan Allah......." Ta sake yin shiru, a hankali ta saki hannayen RAUDA ta hade nata hannayen a hankali ta sake furta" Dan annabi,......Ki yi hakuri ki amince da hadin nan....koda na wata daya ne tak....koda na sati daya ne tak ..............'''... Da sauri RAUDA ta kai hannayenta ta riko na Mah a dan rikice ta ce" Mah" Mah ta katseta tana fadin" Ki bari na roka, dan na san na taro maki rigima, ki bari na roka dan na san abu ne marar dadi, ki yi hakuri ki bari na roka dan a yau yau nake da muradin ki je gidan cen a matsayin matar gidan, YUSUF Sarki ne, sarauta Allah ke naɗa bawansa, tunda ya hau sarauta alhamdulilah yana iya yinsa a matsayinsa na sarki, yana kokarin kare dukkan abinda ya dace, sai dai sarki sai da sarauniya, tasa sarauniyar maimakun ta zamo uwar marayu sai ta zamo makiyiyar marayu, ta kori da yawa ta zagi da yawa, ta wulakantar da yawa..... RAUDA kin san yau da gobe, na san har yanzu bata samu damar da take bane, da tuni ta aikata abinda take da niya, sai dai Ni na san karfin ikon mace a kan namiji, duk macen da ta yi niyar rikita maka lissafi cikin hikima zata saka ka aikata mugwayan aiyuka ba tare da ka ankara ba , saima ta Barka a zuwan kai ne ke tsara komai dan ka isa, bayan ita ke tafe da ragamar rayuwarka, Ni na tabata idan ta samu dama sai ta dama tashin hankalin da garin Tsatsunburum zai hargitse da fitintinu na yau da gobe ......... Daughter..........i bg you, ki amince da............" Da karfi RAUDA ta shige jikin Mah ta rukunkumeta, murya na fita da wani irin sauti cen cikin makogwaro ta furta" Mah, Please ki yi shiru........" Idannuwanta ta lumshe itama ta rungumeta, a hankali ta furta" Mah......., ina dalili zaki ringa wannan magiyar bayan kawai cewa zaki yi ke wance na miki miji ki je ki yi biyayya?" wata irin ajiyar zuciya ta kwacewa Mah, a hankali RAUDA ta sake rungume Mah, a raunane ta ce" Koda mahaukaci ne, ko maye ne, ko marar asali ne in dai ke kika zaba min in sha Allah zan yi biyayya bale wanda kika haifa da cikin ki........, Mah rashin jin sa ya kai nawa ne? koda ya fi nawa nima ai ba jin nake yi ba...., ama a haka kika daukeni tun baki san usulina ba, kika rungumeni kike ciyar da Ni ba tare da jiran na biya ki ba, kike tufatar da Ni ba tare da zagina ba, kika bani muhalli ba tare da mun hada kudin haya ba, karshe kika bani uwa da uba da dangi nawa nima wa'inda nake rayuwa a cikinsu kai tsaye da yanci, shikenan dan ina butulu sai a zauna ana hadani da Allah dan an min miji?......Dan Allah ki daina min magiya kar wani ya ji bayan mu na ji kunya Mah........" Hawayen Mah sai yanzu suka bale, Walahi ta yi tunanin RAUDA bori zata dora tace bata so, ta zata da kyar RAUDA zata amince da wannan magana, sai gashi cikin kudirar Ubangiji yarinyar ta yi mata ba zata har ta sa ta ji wani irin kwarin gwuiwar da ya sakata sakin dariya bayan ta dago ta hannata kukan Mah na dariya tana kallonta ta ce" Allah ya miki albarka, kin ga kwonta huta ina zuwa" Mah ta mike cike da farin ciki ta fice a dakin Mah na fita RAUDA ta sauke ajiyar zuciya ta sada kanta zuciyarta cike da tunani Yau Yau zata tare? ..........kwarai kamar yadda ta nunawa Mah ta karba har cikin ranta ta karba din, kuma maganar tarewar zata je din............sai dai abinda yake dan kai kawon mata a zuciya shine..................ba maganar wani abin bayan wannan! daga shi har matarsa sai ta saita masu zama ne!, domin shima haushinsa take ji sosai da sosai! ________________________________ Damagaran Zaune suke a falonsa, Shaheed da matansa, wato NAJEEBA da Nadia Tun dazu yake waya da YUSUF, su kuwa sunna fira a tsakaninsu, ama tunda ya furta maganar sabon ango NAJEEBA ta yi shiru tana jiran ya gama sun jima sunna yi kamar yadda suka saba sannan ya kashe yana murmushi ya juyo inda suke zaune dan meeting aka hada na maganar fita, sunna so a karra masu yawan fita a wata shi kuwa yace bai san zancen ba Murmushi NAJEEBA ta yi tana kallonsa ta ce" Mai girma bawan Allah, abokinka aure wata da watanni ama ba'a daina kiransa sabon ango ba? koda yake, kaima ai ango ne Yaushema aka baka mu?" murmushin ya yi shima ya ce" Mai girma baiwar Allah jiya fa muka kara masa wata, ina wannan wace mijinta ya rasu? wace Mah ke riko? ita muka bashi jiya" Dif ta yi tana zarro idannuwanta, a hankali ta ce" Aban MUHAMAD kana nufin RAUDA?" Shima ido ya dan zuba mata dan jin ta kama sunnan cirat kafin ya gyada mata kai Kai ta dauke tana murmushi hadi da dan kada kafarta a ranta ta ayana' Masha ALLAH, yanzu sakon Amnah take ko wa ya zo daidai lokacin da ya dace ya zo, fita kuwa yanzu zan yake ta oga dan idan da hali yauma ka barni na je na yi Allah sanya albarka a wannan aure, domin yanzu Sir YUSUF ya yi aure mai sunna aure?' Da wannan suka ci gaba da tattaunawa tsakaninsu na tsayar da mafita......... ___________________________________ Tunda tashin busa da hayaniya ke tunkaro dakin Mah gabanta ya ringa dokawa a gudun da ya wuce ka'ida, shi yasa ta yi tsuru ta zubawa Kofar ido har aka bude Hajia ta fara shigowa da sandarta a hankali, sai matan da aka yiwa lakabi da matan daraja wa'inda suke na darajan domin sukan halarci taron daraja ne, hannayensu dauke da akwatuna masu ɗauke da alkyaba da tufafi da kuma takalmi da sarka na gidan sarauta Daga bakin kofa masu busar suka tsaya, sai dai tamkar a dakin suke busawar dan ita tuni ta nemi rikicewa, bale da ta ga niyarsu bayi zasu kaita, da girman nan nata wani saka lalle ne zasu yi mata, ko sun manta shekaran jiya ta gama takabar wani mijin da ta aura ko menene?, ko kuwa tarin girmansa ake son karra jaddada mata aka yi hakan da ita?, ita dai ta san wata irin juwa da tashin tsigar jiki suka hannata gane inda za'a nufa da ita, kuma me ake nufi da ita, har aka yi mata rabi da rabin wanka domin kuwa sket dinta a jikinta da karamar riga firrr ta rike su kanta a sade, hakan ya sa matan suka kalli junna suka sakarwa junna murmushi harda Hajia wace wani irin farin ciki ya sake lulubeta ta mika hannu ta karra daukan wata takarda a gefenta ta kara a wace ke gabanta wani irin turare mai sansanyan kanshi suka yi mata wanka da shi, sannan suka karbi bra da pant din da Mah ta miko masu suka bata, Rauda kuwa da ta karba sai da ta shige bayi ta saka dan kunyarsu ta fi komai damunta a yanzu.................. 56 Bayan ta saka din ta labe a bayin har sai da aka fitar da ita tana ji tana ganni su suka shiryata sannan suka zaunar da ita a bakin gadon nan, daya daga cikinsu tana murmushi ta ce" Girma ne, daukaka ce, daraja ce daga Ubangiji kasantuwarki mata a wajen MALEEK, Allah ya karra maki lafiya da nisan kwana, ya sa muna da rabon gannin tsatson ku ke da MALEEK......." Sai kawai ta ga iyayen matan nan sun kai zaune a wajen kawunnan su a kas A rikice ta dago ta kalli Hajia tana kokarin tashi, sai ta ga Hajiar ta girgiza mata kai itama ta dan sasabto daga kan kujerar ta dukar da kanta a gabanta Gaban RAUDA ya karra faduwa, da sauri ta taso ta zo gaban Hajiya ta duka kanta a kasa muryarta na rawa rawa ta ce" Hajia, dan Allah ku rufa min asiri ku dago kanki, Hajia" Hajia ta dago tana murmushi ta kama hannunta a tausashe ta ce" baki san daraja ce Allah ya yi maki ba? a gabannan zaki ringa gannin manyan mutane na dukawa dan gaisar da ke, bale idan kin yi hali na gari, Allah ya baku zaman lafiya jikata, koma ki zauna dan daga yanzu har zuwa dare masu zuwa gaisar da ke ne zasu yi ta shigowa, dukkan wani abinda suka baki kawarki Bara'atu dake waje ita da Salima zasu amsa su adana har a zo daukan ki, a yau ba za'a yi maki kitso da kunshi ba sai kin yi sati Daya cir a gidanki, idan an kai ki zaki samu lokacin karantar rayuwar mijinki da taki kanki, ki kwontar da hankalinki, ko me kika ga ya shige maki duhu ki nemi mamanki ko ki zo wajena, Allah ya yi maki albarka AMEERAH...(SARAUNIYA)" Kai ta sake sadawa cike da jin kunya da nauyin Hajiar da kuma matsanancin tsoro na abinda yake wakana a gabanta mayar da ita suka yi mazaunin ta, aka kawo takardu biyar cif aka ajiye babar cikinsu ta ce" Wannan kyautar Barka da zuwa ne daga kakar MALEEK, takardun manyan filaye ne a anguwar gayu har su biyar , kowani fili ana iya yin ginnin tankamemen gida da masalaci da shagunna a jiki, Allah ya taimaki Ameerah RAUDA tabas kin fara da goshi" Ita dai kanta a kasa har suka gama suka fice sannan ta ji Muryar su Atu sunna ihun da ya sa ta done kunnayenta ta kwonta ta rukunkume alkyabar da aka saka mata, suka ringa ja ama ta masu banza ta ki tashi, har sai da Mah ta shigo suka nutsu suka bata lafiya, Mah kuwa ta cenza shiga ta dau wanka ta sa aka kawo masu lafiyayen abinci sannan ta fice tana fadin" Ina zuwa, zamu zauna da iyayen Amnah ne dan an sanar masu yau zata tare , Please kar a yi wasa da Sallah da kuma abinci dan baki ne da Ni sosai, kuma ku kiyaye duk sakon da aka kawo kar ku hade waje daya kuma ku kula da masu baku sakon, saboda ta haka an shigi Ameerah da yawa da suka shude?" Karshe dai a dole suka kyale RAUDA, saboda duk yadda suka so su zanta ta kiya, Atu kanta ta bata dama ta kyaleta da maganar sai sun yi fira, ta sakawa ranta zasu yi ne daga baya, abinda ya kwontar musu da hankali su Dukansu bata wani koke koke, ta sakawa ranta hakuri a yadda ta nuna masu su duka Cikin sama da kasa da tarin hargitsi aka yi wunin nan, domin a wajen su Rauda kadai aka yi shi shiru shiru, wajen iyayen RAUDA sun nuna bacin ransu ainun na yiwa y'arsu kishiya tun bata tare ba, hakan ya sa Hajia ta nuna masu ta fi su duk wani abinda suke tunanin sunna takama da shi , karshe aka yi rabuwar ba dadi dan kuwa sun tafi ne ba tare da sun samu abinda suke so ba, dan Hajia bata yarda da maganar da ake fadi cewar mahaifin Amnah ya riga ya zama hotiho ba sai yau da ya zo da abokinsa suka yi maganar basu ji dadin yiwa Amnah kishiya ba, bayan tafiyarsu dariya Hajia ta yi ta gyada kanta ta sa aka leko mata wajen Amnah aka sanar mata Amnar na nan da kawayenta uku, hakan ya sa ta basar ta ci gaba da shagulgulanta har dare ya yi aka yi sallar isha'i aka gama Ana gama sallar isha'i Mah ta sake dinkewa da y'arta, tamkar wace za'a kai wata kasar ko wace za'a ba wani bakon ba wanda aka sani ba haka Mah ke karra yi mata nasiha da fada mata ko meye ta gayawa Allah kuma idan ta ga ba hali ta gaya mata kawai dan ba zata yarda a cuta mata ba, ita dai kukanta take sha, tamkar wannan auren ne aurenta na farko, tarin mutanen da suka zo rakiyar ta kuwa sai da ya tsorata, Hajia ce da kanta a gaba, aka yi mata rakiya har falo baba, daga nan Hajia ta kaita da kanta har part dinta ta zaunar da ita saman kujera sannan ta karra yin abubuwan tsarin da suka amso ta sake jaddada mata rikon azkar da Adu'o'in tsari a kowani motsinta sannan ta fice tana mamakin ba Amnah ba labarinta, ta tatara jama'arta suka tafi tana dokawa YUSUF kira dan ta shaida masa ya san da ya je ya duba kowace kuma ya zama tsayaye a gidansa kar a cutarwa RAUDAH, har fadi take yi yarinya bata cewa komai sai ido kar a je a zazageta ko a taba lafiyar jikinta dan ita ba yarda zata yi ba shi dai bai ce komai ba dan a lokacin yana cikin buga basket ball ne har a Damagaran suka yi salama ya ci gaba da bugawar, ama hankalinsa a rabe, a dole ya yi masu salama , dama basu wuce su takwas a filin ba , ya su ya su ne ba ya mu ya mu a ciki gaskiya ......ya yi tafiyarsa A nutse Taj ke tuka shi har suka karaso kofar baya, ya sauka bayan sun yi yar gajeriyar magana ya nufi kofar ya bude da ky din wajensa ya shiga ya rufe a nutse ya kama hanyar falo baba , jikinsa sanye da wandon da ya dara gwuiwa da kyar, rigar kuwa mai yankaken hannu ce, damatsunnan hannayensa da kwaurinsa duka kaf a waje sai motsi suke yi su kadai saboda cika da koshi, gashin kansa kuwa ya fito ya yi sidik a kan nasa A hankali ya dakata jin Muryar AMNAH da karfi tana fadin" Magana nake yi maki y'ar matsiyata, Ai shine harda fitowa daga wancen akurkin da aka baki kika zauna min a baban falon gidana? ki sani kin sanyo kanki kurkukun ukuba dan sai kin gwamace kida da karatu, sai kin nemi a amshe ki kar na kashe ki, dan walahi da hannayena za.......................kukukukukukukuku wayo ALLAH kan uba, ke Ni kika innalilahi ke!" Magangannunta suka ringa cenza salo kamar mai aljannu, karshema sai ya ringa jin karar abu kamar duka dai kamar kuma dai wani abin daban da sauri ya karaso yana baza idannuwansa a falon Ido ya zarro sakamon ganninta dodar a saman ruwan cikin y'ar mutane ta hade hannayenta tana yi mata tankadeta mareta da dayan hannun mai haɗe da naushi ido ya sake zarrowa ya shigo da sauri ya duka ya cicibeta ya dagota da karfi ya...... Hello people, fatan kunna lafiya,shin kin karbi bonanzarki kuwa? a farashi mai sauki na saka aunty, TUNTUBENI a numbana kamar haka 93811618......ki amshi NOVELS DINA a kan 1k in sha Allah....thank you 57 Azl 58 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo Ido ya sake zarrowa ya shigo da sauri ya duka ya cicibeta ha cirata da karfi ya dagota daga kan ruwan cikin y'ar mutane kuma matar mutane, sai dai bai sani ba ta riko rigar daf hakan ya sa ta janyo rigar Amnah kiiiiikikik ta yaga gaban sannan kafin ya idasa janyeta a jikin Amnar sai da ta sakar mata kafa Sauketa ya yi yana kallonta da mamaki zai yi magana ta sake yin kukan kura ta karra yin kan Amnah, hakan ya sa ya furta" Lah......" Yana sake fido idannuwa Ihu AMNAH ke yi wanda ita da kanta bata san har ina girman amon muryarta ke zuwa ba, ita dai ihun da take yi na duk wani wanda zai iya jinta ya ji ta ya rabata da mahaukaciyar nan ne tun kafin ta rabata da ranta A haukace ta kama hannunsa da ya riketa taf yana kallonta ta saka bakinta ta dantsa masa cizo Ido ya rintse dan har ga Allah cizon sai da ya ratsa shi sosai , kai jama'a kiris ya rage kato ya saki y'ar nan ya zunduma ihu, Allah dai ya sa ya kai dayan hannun ya talabi keyarta ya rike yana kallonta bayan ta janye bakinta tana kallonsa dan gannin ya ki sakinta Karra bude bakin ta yi, da niyar sake dandana masa azabar da ta dandana masa yanzun nan, a yanzu kam lokaci daya ya ja tunga da ita a rike a hannunsa ya sake kama hannayenta ya cirata ya nufi dakinta da ita Ihu take yi a yanzu, dan tun dazu bakinta a jimke yake, tana harba kaffafuwa tana ihun ya sauketa, ama ya kiya sai da ya kaita dakin ya karasa wajen gadonta ya dagata ya timata a saman gadon A zabure ta mike ya kuma daukanta ya timata a saman gadon yana sake kallon y'ar nan da wani balagagen fitina dake sake tsimkota niyarta kuma mikewa, dan wani tsohon neman isgili idonta idonsa ta ce" Ka barni, ka barni sai na zaneta walahi!' Ido ya sake zarrowa yana kallonta ya ce" Ke to y'arki ce da zaki zane ta?" Ido ta zuba masa tana mamakin yadda daukanta baya ce masa komai, ta dafa ta zauna tana furta" Wash Allahna bayana, yanzu tarayya zaku min kai da matarka ku karya Ni?" Shima idon ya zuba mata, irin yadda ta marairaice muryarta tana nuna masa zasu mata tarayar sai ya rasa irin kallon da zai yi mata,......gaba daya ta yi kamani da kyakkyawar fulawa mai kyan kallo, a hankali ya ce" Ki ji tsoron Allah RAUDA, me ta maki ne?" Kai ta cire daga dubansa tana mikewa tsaye gaba daya, hakan ya sa ya yi saurin tsayawa a kan hanyar kirjinsa ta bi da kallo yadda ya yi mata kikam, kuma ta san ko a kashe sai ya kasheta ya birne babu wanda zai sani, hakan ya sa ta ja baya ta bude murya rai bace ta ce" Allah ya isana Ni da ita, kai kuma ba'a yi dacen mace ba, na zata zan ga wata zukekiyar mace a gabana ne, sai na ga wancen abar, kuma walahi haduwa koma fitar da raini goma tunda ta raina min iyaye, ita ta isa ta zagar min uwa? ita din banza? duk wanda ya yarda ya zagar min ita sai inda karfina ya kare, aikin banza,, na rantse idan na kuma ganninta sai na kumbura mata fuska!" "Ke zo nan, zo nan!" YUSUF ya fada yana sake zarro ido da kallon bakon balaki yau shi Yusufa jikan Muntari, duk inda yayi tunaninta ta wuce nan ashe? kuma idonsa idonta tana cewa wai za'a yi mata taraya Baki ta turo ta shige bayin da sauri ta rufo tana sake tunzuro bakinta a ranta ta ayana' Ba zan zo ba, kuma yau Ni da ita shege ka fasa, aikin banza mai kama da munafukai!' Ya jima a tsaye, ya rasa abinda zai yi, kofar bayin yake kallo , a ransa yana tunanin ya bani yanzun yaya zai yi da wannan fitinar?, da kyar ya juya daga dakin yana tuna maganar Hajia ta dazu da take fadin yarinya saliha da ita bata cewa komai sai ido idan aka yiwa jikarta wani abin ba zata kyale kowa ba...... A bayane ya furta" Hum!" Bayan ya fito ya yi tsaye ya ga ba Amnah ba labarinta A nutse ya nufi dakinta, dan ba zai je ya kwonta haka ba kar aje wancen rigimamiyar ta yi mata ilar da ake iya yi mata shari, dan haka ya je ya kama kofar ya murda ya shiga a hankali ya dakata yana kallonta ta baya yadda take tsaye tim da ita bata da komai a jikinta tana waya da mahaifiyarta tana sheka kuka da zayane abinda ya faru Idannuwansa ya dauke daga kanta ya juya ya fice a dakin ya ja ya rufe a hankali ya nufi kujerar nan baba ya zauna ya shiga yamutsa gashin kansa kirjinsa na neman cenza masa yannayi Dan murmushi ya yi a hankali yana girgiza kansa...., a ransa yana tunanin ai ba laifi an jima ba'a sadu ba, idan yanzu an ji dan alamun bukatar hakan normal ne, sai dai koda shi maye ne wannan naman ba abincin cinsa bane, bai taba tsana da kyankyamin nama ba sai a kan wannan, tabas a kan wannan naman ya gane ashe shima yana da haram a duniyar nama Murmushi ya sake yi ya mike ya nufi dakinsa,, dan wanka yake so ya fara yi kafin komai, ga yinwa yana ji, ga gajiya kuma ta kokowar nan da ya karra yakan yi murmushi ne kawai ya fitar da sautin Hummmmmmmmmmmmmm, shi da kansa ya gama yarda cewar kamar kumbo kamar kayansa ne Da sassafe kusan karfe bakwai daga daga masalaci ya wuce bangaren Hajia, ya sameta a falo zaune tana ta fama da turaran wuta a cikin hijabinta ko tsoron ya kama mata hijab bata ji Zaunawa yayi yana shan kanshinsa da yake yi mata kwana biyun nan, ita kuwa sai faman masa sannu take da gaishe shi kamar shine baban ba ita ba Ciki ciki ya ce" Abinci nake so" Hajia ya zuba masa ido tana kallonsa, abinci kuma? ita batama san me zai fito da bawan Allahn nan ba da safiyar nan ya zo wajenta bayan ga y'ar mutane cen an kai masa Baki ta dan tabe ta mike da kyar tana fadin" To bari in ha ko sun gama girkin, ama kuma na zata ko ka yi hakuri a kai maku cen din kar ka ci ka bar baiwar Allah marainiyar Allah, gashi ka barota ita kadai kar aje wannan fitinaniyar matar taka ta tarda min ita ta yi mata wani abin, dan Ni walahi Amnar nan tsoro take bani" Har ga Allah sai da ya kalli Hajia bai shirya ba, kafin ya saki murmushin da bai shirya ba yana gyada kai hadi da dan cije lebensa ya mata shiru Hajia ta kauda kai a ranta tana ayana' Oh, d'an nan sai ya ringa wani abu kamar wanda ke dauke da wasu halittun bayan bil'adama, bari a hada a kai maku cen din dan ba zan so ka jima a nan yau yau ba ake ta tarda baiwar Allah ta yi mata wata ilar ba!' Yana nan zaune dogari baba ya karaso ya yi salama sannan ya tsaya yana jira a bashi damar shigowa Jakadiya ya sanarwa Hajia wanda ke salamar hakan ya sa Hajia zuwa falon ya bada damar a shigo da shi Shigowa ya yi ya zube kasa kansa kasa ya shiga kirari gannin YUSUF din a falon, har sai da ya dakatar da shi sannan ya yi shiru kansa a kasa ya ce" Allah ya taimaki kakar saraki, dangane da dokar da kika dora ne jiya cewar gabanan kar a ringa shigowa yadda aka so dan ana takamar an shafi gidan nan dan ana aure a gidan, to tun jiya kusan karfe daya na dare baki suka zo muka hanna shiga, da kyar suka koma sun ce ne wai iyayen Mai baban daki ce wato gimbiya ta farko, to yau ma sun dawo tunda duku duku sunna kofa mutane hudu ne da mata uku da wani akace mahaifinta ne, wai ance bata da lafiya ne sunna son shigowa shine nace bari dai na sanar maki kar mu hanna su shigowar aje abin mai mahinmanci ne" Hajia ta kalle shi da kula ta ce" Wai kanana nufin iyayen Amnah?" Ya karra sada kansa yana mai tabatar mata su din ne Hajia ta rafka salati tana tafa hannu ta ce" Yau na ga balaki, uban me kuma ya dawo da mutanen nan gidan nan yau? Yau na ga dangin mahaukata haka zata yi zaman auren? a'a fa, ba sai yiwu ba, a kira min Jakadiya a je da baba baba a hadata a kai masu ita, idan sun shirya barinta yin zaman aure sa dawo da ita ta yi zaman aure!, ba zai yiwu ba, a kirawo min duk wani mai isan isa a gidan nan, bata isa ba walahi, kuma duk isar iyayenta basu isa ba , ba dai a fadar TSATSUNBURUM ba!" Ta karashe ranta bace hadi da daga muryarta, da sauri ya mike bayan ya bayar da hakuri ya fice a falon ita kuma ta zauna ranta na tafasa tana kada kafa Da ido yake kallonta, yana mamakin rikici irin nata, tsofai tsofafi sai iya daga murya bata ko jin wahalar ihu idan ranta ya bace Dan murmushi ya yi ya sake gyara zamansa a nutse ya ce" Ta yiwu fa da gaskiyar zuwansu fa" Hajia ta lalle shi da sauri ta ce" wace gaskiyar zuwansu kake fadi ranka shi dade?, wace gaskiyar zuwa? basu da dalilin da zasu nemi zuba min raini a nan, jiya fa ubanya ya zo nan da maganar dan mi za'a yi mata kishiya ko shekarewa bata yi a gidanta ba, walahi yana maganar idan ka kalle shi kamar mahaukaci, Ni kuma na tuna masa shima ai auren ya karra ba iya uwarta yake aure ba, kai dai abokinsa da suka zo tare ya koma yake bada hakuri da fadin dan Allah a yi hakuri shi bai san abinda ya kawo su kennan ba da ya hanna, Ni dai ban raha masu ba na masu sumul, me suke tunani , yau da ace wata y'ar a yi kwatance ce suka bamu sai ace masha ALLAH, ama y'ar da ita da banza shashasha duk daya, mtssssss Ni dai an bani abu a rufe ana ta cutata a banza a wofi!" Murmushi ya sake yi a nutsensa ya ce" Kar ki ga laifinsa, y'arsa ce ai, kuma kin ga kar ki sa a kore su baki yi bincike ba, tam, dan kin ga salihar jikar nan taki? jiya zane min mata ta yi kamar ita ta haifeta!" Hajia ta sake dubansa da kula da yannayin tashin hankali ta ce" Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, Kana nufin jiya Amnah din ta dakar min RAUDA?" Sai da ya karra yin murmushin nan da ya ki barin zuciyarsa ya gyara zama ya girgiza kai ya ce" A'a, ita dai baby din ce ya zanne Amnah" Hajia ya zuba masa ido, gaba daya gani take yi kamar baya ganewa, dan haka ta dan matso sosai kusa da kujerarsa tana kallonsa ta ce" Baka gane ba fa, ita Amnah itace y'ar wadinncen mutanen , ita kuma baby itace wace aka aura maka jiyan nan wannan y'ar karamar da bata cewa komai, yarinyar nan fa ya wajen Mamanka fa nake nufi, itace ai RAUDA ko?" Tsakani da Allah sai da ya ji dariya ya kama masa zuciya, ya girgiza kai yana kallon tsohuwar nan da wani tsukaken bakinta irin na tsofi, to shi in ba garaje ba waye zai ce masa wance ce Rauda? ai sai dai ya gaya maka wace ita da sauransu yana kallon ya ya ce" 😍😍😍😍😍😍😍 yana kallon Hajia ya ce" Ita dai jikar taki ce ta zane dayar" Hajia ya yi shiru tana nazari, sai kuma ta sauke ajiyar zuciya ya juya ta je bakin falon inda Jakadiya ke tsugune tana jiran abinda za'a fadawa dogari da kuma wani sakon idan akoy A nutse hajia ya ce" Ki ce a basu damar su shigo, sannan ki isar da sakon ina son gimbiya Amnah da gimbiya RAUDA su halarci falona" Kai a kasa ta amsa da" An gama kakar saraki" Sannan ta mike ta wuce Jiki sanyi Kalau Hajia ta koma ta zauna tana kallonsa irin yadda ya gyara zamansa yana cin tufa hankali kwonce, ta zatama zai yi tafiyarsa ne, sai ta ga ya zauna,, ba zata so a ringa irin shirmen nan a gabansa ba, dan kuwa ba zata so ya yanke wani hukuncin abinda ya shafi iyalinsa cikin fushi ba Shi kuwa zaunen da ya yi, ba komai yake son ganni ba sai wayewar gari da idon da zata kalli mutane ita wancen da ake kira marainiyar Allah, yakan yi murmushi ya girgiza kai, duk irin ayyukan dake gabansa baya jin zai iya zuwa ya yi idan bai ga abinda yake son gani ba, bashi da niyar furta masu A a zaman nan, ama kuma ba za'a hannawa ido kalaci ba Su suka fara shigowa bayan an bada damar su shigo baban falon Hajia Abin mamaki yau dinma shi da abokinsa din nan da kuma matarsa, wato mahaifiyar Amnah Tunda suka shigo Dogari ya nuna masu wajen zama saman baban cafet din dake tsakanin cafet din da ƙafafuwan YUSUF ke sama da kuma kujerar da Hajia ke sam,, suka zauna idannuwansu suka sauka a kan YUSUF kusan kowane ya karra kama kansa harma suka so manta abinda ya kawo su Daga kofar shigowa dogari ya koma ya tsaya bayan sun gaishe da Yusuf da Hajia Dogari ya yi aikinsa ya nuna sun amsa, Bama kamar Yusuf da ya saka Tissu ya goge bakinsa sannan ya dan zuba masu ido kadan kafin ya dauke kansa yana murmushi, gasu dai cikin shiga mai kyau, sai dai a cikinsu kowane da abinda.ke.tafe da rayuwarsa mai hatsarin gaske wanda idan bawa ya ji sai ya firgita Hajia kam abokin nan na Mahaifin Amnah ta zubawa ido, da wani kallon da ya saka shi sada kansa yana jin kirjinsa na sake dokawa, domin dama tunda suka shigo ya ga YUSUF ya ji hankalinsa na neman tashi Kai Hajia ta dauke a zuciyarta tana cikin mamaki mai tsananin gaske na kamanin da wannan bawan Allah yake yi da Amnah, kamanin har sun bace sosai, sai ta sakawa ranta ta yiwu da akace abokinsa ne ko d'an uwansa ne na jinni kuma abota take da karfi a tsakaninsu?........., ita dai ta ture tana duban su da kula ta ce" Shin me yake faruwa haka ne? ance jiya wajen karfe biyu kun zo, gashi yau tun dazu kuke kofa, Allah ya sa lafiya?" Kan mahaifin Amnah a kasa, yana jin abinda Hajiar ke fada ama tamkar wanda ya afka wata duniyar tunani daban, har sai da abokin ya sake tabo shi ya ce" ana magana baka ce komai ba Elhaji?" Da wata irin murya, wace kana ji sai ka kalli mai ita duba da Muryar sama sama ce kamar baya cikin hayacinsa ya yi maganar , irin sama sama din nan ya ce" Eh, haka ne, dole zan zo da duk wani wanda ya isa da yata, dan ba zai yiwu a kashe min ita ba kamar yadda Hajia tace ko ba haka ba hajia?" Ya karashe yana kallon mahaifiyar Amnah da hannayensa bibiyu a hade kamar wanda ke rokonta wani abin, ita kuwa ta sake sada kanta yadda ka san irin manyan salihan matan nan da ko surutu da karfi basu iya ba bale ace zasu aikata mugun abu Shigowar dogari da sauri yana fadin" Kai, ka sasauta muryarka a nan wajen ko ka fito mu iya da kai talaka!" Ya sa YUSUF dago dubansa ya masa alamun ya fita da hannayensa, da sauri ya juya ya fita din yana jin tamkar ya warto mahaifin Amnah ya koyo masa hankali, dan ba'a yi wanda zai yiwa MALEEK magana haka a gabansu ba tare da sun datse harshensa ba walahi! ya godewa Allah ba Taj bane a wajen dan kuwa shi bashi yake bi kuma sai an biya shi! Sake gyara zamansa ya yi a lokacin da Mah ta shigo tana kallon iyayen Amnah da mamaki ta karasa ta duka ta gaisar da Hajia, sai dai Hajia bata samu damar amsa gaisuwar ba saboda ranta ya kai kololuwar ɓaci ta budi baki da fada ta fara fadin" Ohk, shine kuka kwaso jiki kai da d'an uwanka da matarka kuka zo ku shiga fadan tsakanin abokan zaman da fadan bai yi tsauri ba , dan ita Amnah itace mai gata ita kuwa RAUDA bata da kowa ko? To ai RAUDA ita keda gata, wanda bana tunanin Y'ARKU tana da shi, domin ga Mamanta nan, Ni kuwa nice kakarta, !" Gira ya dan dage yana kallon Hajia kasa kasa ya furta" Ko?, to wa yace maki d'an uwansa ne? ba hadinsu fa" kallonsa Hajia ta yi, domin idan ba ita dake daf da shi ba babu wanda zai iya jiyo abinda YUSUF yake fadi, da sauri ta kalli bakon , ta sake kallon YUSUF daidai lokacin da AMNAH ta fara shigowa da abaya a jikinta fara, tana gannin iyayenta ta je da gudu ta fada jikin mamanta tana fashewa da kuka, ita kuwa Hajia abinda ya fito daga bakinta tana kallon abokin mahaifin Amnah ta ce" A'a fa, d'an uwansa ne mana, bawan Allah kai ba d'an uwan mahaifin Amnah bane? haba wannan kama ai sai jinni, sai kace a tatsuniya ai ba za'a ce tsabar abotaka bace ta sa y'ar nan ke kama da kai ko?" Da karfi mahaifiyar Amnah dake sune sune tana ba Amnah hakuri kasa kasa ta dago ta dubi Hajia, kuma wani ikon Allah a tare suka dubi Hajiar sannan suka kalli junna, da sauri ta budi baki tana fadin" Ke Amnah yi shiru mana, ya isa haka, ke ashe fada be kawai kuka yi ke da abokiyar zamanki, wannan ai ba wayo bane, ina mijinki yake da zaki wani kiraye mu? haba dan Allah Ni bana son ka zama mutun marar sirri, duba ki ga mahaifinki ko ido bai rintsa ba tunda kika kiraye shi kina kuka, na yi na yi ya yi hakuri ko menene ke da kike gaban magabata an yiwa abin tsawa kika kiya, haba Ni na ji kunya walahi kin sa mun zo gaban iyayenki da wannan maganar, Hajia dan Allah a yi hakuri a yafewa yarinta, kin san ita Amnah bata iya fada ba , sam bata san rikici ba, kunu huce in shaka sunnan Amnah fa, tsorota ta yi da y'ar uwar Tata shi yasa ta rikice, ama gabanan ai ko wani abin ne ga mijinsu sai ya yi masu shara'a ya sasanta su, in ba iya shege ba RAUDA kanwarta ce ai ba wani maganar kishi, Elhaji mu je haba ka huta bawan Allah gajiya ta ishe shi ita ta zo tana wani damun mutane, ku mu je" Ta mike tana mintsinin cinyar Amnah, wace ta dago tana kallonta da mamaki a bude fuskarta da kyau dan ta ga irin yadda jinni ya kwonta, har bata ga shigowar RAUDA da salamarta ba dan tsananin mamaki tana gannin yadda mahaifiyarta ke mata alamun su yi waya da irin yadda ta kada mahaifinta suka tafi komai ba'a yi ba, komai ba'a yiwa wancen mahaukaciyar sauvage din ba, duk irin abinda ta yi mata? a rikice ta juyo bayan sun wuce , hakan ya sa dan kwalin abayarta faduwa daga kanta ya sauke daga rufewar da ta yiwa fuskarta Ido Hajia ta zarro tana kallon fuskarta ta ce" Subahannalahi ke, meye wannan a fuskar ki kamar wace mota ta bi ta kai? kaikaikai rufe rufe wannan tsaba tsaba wajen kuncinki hala wani tautau ya zuba maki ruwansa a kanki? subahanallah...." Mah ma dake murmushin inda RAUDA ta je ya zauna kanta a kasa tunda ta shigo da wani zumbulelen hijab tamkar zai makata a kas dan ya yi mata yawa sosai kuma kan nan a kasa ta ki dagowa ta kalli kowa ta dubi Amnah itama tana fadin" Subahanallah me ya samu fuskarki haka? ko wani abu kika shafa ya kumbura maki fuska?" Amnah ta girgiza kai tana matse kwallah ta dubi RAUDA tana jin da ace za'a bata bindiga walahi tana iya harbe RAUDA har lahira, sai dai ba laifi wasan yanzu aka fara shi dan walahi sai ta rama, ta fashe da kuka tana fadin" Walahi babu abinda na shafa, jiya ne kawai na fito baban falo dan na yiwa honey sannu da zuwa wannan ta sandeni ta duka min karfe a wuyana ta shiga dukana da abubuwa, ba iya fuskata ba harda jikina du birdi ne, birdi ne wannan din ai na abin duka" Ido suka karra zarrowa, kamar an juyar da dubansu suka kalli RAUDA wace itama ta zarro nata idannuwan jin wata rantsatsiyar karya tana kallon Amnah da yannayin mamakin nan a ranta ta ayana' ok, na zata ai gaskiya za'a fada har na tsorata, tunda karya kika zaba fine' A fili ta ce" Ni wai kike nufi aunty Amnah? innalilahi wannan jikin naki duka to da me? ina Ni ina ke aunty Amnah da zan iya ko dukan ki ko me? innalilahi wannan me ya same ki haka?" Ido ya zarro lokaci daya ya kai hannunsa wajen bakinsa a hankali ya furta " Lah " Ita kuwa Amnah sai ta ji kamar zata summa ɗan tashin hankali, mikewa ta yi da sauri ta shiga dage abayarta har wajen cinyarta da duwawunta hankali kwonce ba tare da ta yi tunanin hakan wai wani abin a ji kunya bane a gaban iyayenkama bale sirikai, ita dai burinta su yarda da abinda ta fada tana duban RAUDA ta ce" Kar ki raina min wayo kin ji, kin yi kadan na maki karya kin ji? kina nufin du abin nan da kika min baki san kin yi ba? to ko aljannu gare ki baki sani ba? wannan ai karyar banza zaki yi munafuka kwarariyar yar iska.........'" "kin ga, Amnah ke, zo nan zauna, kuma ki kiyaye wasu furucin a nan dan ba zan dauka ba!" Hajia ta fada da karfi, hakan ya sa Amnah zuwa ta zauna din sai kumbura take tana kallon RAUDA tana harare harare Hajia ta dubi RAUDA ta ce" RAUDA kin san wani abu a kan abinda take nufi? kin doka mata karfe sannan kika shamaceta?" RAUDA ta girgiza kai tana kallon Hajia sannan ta mayar da kai ta soke, a ranta tana ayana' A'a kam , ban rotsa mata komai a kai ba, kuma ba fadan shanmata bane tana kallona ina kallonta kuma belt din wandon jikinta ne ai na tatafka mata sai dan marinta da ba yi!' Hannu ya sa yana shafa gemunsa yana kallon makaryata biyu a gabansa, kuma matansa abinsa baki ya dan cije yana kallon RAUDA da ta soke kai, ko shi da ace ba shine ba idan ya kalli wannan innocent face din ba zai taba cewa zata aikata ba, sai dai ga shima shedar ta aikata din a jikinsa fa, kuma jira yake alkaliyar ta nemi Shedu zai gabatar da sheda tabas! Ajiyar zuciya Hajiya ta sauke tana dubansu a tausashe ta ce" Yaushema daren ya yi bale har a kai loma a hanci?, Ni baban abinda yake bani tsoro gani nake yi kamar ja gaban da ya dace ace ya ja gaba a lamarin gidansa bai damu da gidan ba" Ta karasa fada a tausashe tana sauke dubanta a kan MALEEK A hankali ta ce" Ka yi hakuri Allah ya ja da tsayin rai, komai daga farko ake farowa, kuma komai girman mutun da darajarsa in dai magabantasa na raye dole za'a ringa shiga huruminsa koda baya so," Ta sake ajiyewa tana kallon sa, a tausashe ta ce" Koda da zabin da kake hange a duniyar ka a nan gaba, dole ka kiyaye yanzu saboda gobenka, MALEEK ya zama wajibi ka dubi gidanka komai girman abinda ke kanka ka basu lokacinka ka daidaita fitintinnun dake tashi mararsa ma'ana ka sauke dukan hankin dake kanka nasu sannan ka zame masu kariya na zama a rayuwar duniya!" Ta karashe tana kallon Mah, wace ita dinma shi take kallo, kuma sun ga ya sada dubansa alamun dauka yake yi maganar da ake yi masa Hajia ta dawo da dubanta wajen AMNAH, a tausashe ta ce" Haba Amnah, ko me yake faruwa a tunanina mu zaki fara gani idan kin ga ba'a yi maki adalci bane zaki nemi iyayenki, ....domin a sanina idan iyayen mace suka shiga lamari ya bace ne, ko ba haka ba?" Amnah ta kalli Hajia, ita idan ta kalli Hajia tsoronta take ji a ranta, bata tunanin zata iya wata fira da tsohuwar nan dan tsoro take bata Hajia ta ci gaba da fadin" Zaman kishi muka yi da mata kala daban daban a rayuwa, ba wayonmu ko dabarar mu suka kwace mu ba, domin an yi zamanin da mu da miji sai ido, muna ji muna gani miji ya fi karfinmu dan a lokacin ya auro mana shu'umar da ta sa ya dawo gannin munin mu, to idan zama ya yi zama dama an yi haife haife da sauransu kai da miji ai sai kyautatawar yau da gobe, shi kuwa yayi nasa rawar gannin ta hanyar nuna diyauci da darajar da iyali, ama ba wai ci gaba zai yi da gannin mahaukacin kyan nan naki da kike takama da shi ba , komai kyan naki, ki dauki misali a kankin kanki, zaki ga kina son wani abu ki siya, kafin ki siya irin zumudin da kike yi da tunanin idan kika samu ai shikenan kin gama siyan wani abin kuma ɗan wannan din karshe kennan aka baki, sai ki samu ki siya, a hannunki fa abin yake zaki ga wani lokacin ko sati bai cika ba kin rage zumudinsa, wani Sa'in kuwa kikan dauki watanni kamar biyar kina daukinsa, daga baya zai zamo abu da yake da daraja sosai a wajenki kike rike da shi kam da kam, ama ba wai wanda ya fi kyau ko ya fi birgeki ba, idan da zaki samu wani siya zaki yi ki karra ba tare da kin bada naki ba, Amnah haka rayuwa take tsakaninmu da maza, ke matar farko idan har baki iya takunki ba sai kin rasa wannan babar darajar da muke da ita kina ji kina gani, da wannan nake baki shawarar ki yi hakuri, ki iya kawar da kai, ki koyi halaya na manya, ki kasance mai dauke da darajar da mijinki zai rike ki taf, da kishin ba wani ke wato rabuwa da ke, koda ya ga wace ta fi ki a idannuwansa, ta haka zaki fi jin dadin gwagwarmayar rayuwa da rigingimun yau da gobe lami lafiya kin fahimta? ki yi hakuri ku zauna lafiya ke da mijinku da abokiyar zaman ku" Ta karashe tana kallon RAUDA, wace har yanzu kanta ke kasa, ita fa har yanzu gani take yi ko tsokanarta MALEEK ke yi dan Allah? wannan abar tausayin me ta sani baiwar Allah harda za'a ce ta daki wannan da idannuwanta ke kiririta? Sai ta samu kanta da fadin" Zo nan , taho nan in ji" RAUDA ta dago a hankali daga jikin Mah dan tun dazu Mah ta sa ta dawo daf da ita, ta kalli Hajia ta ga eh da ita din take, dan haka ta mike a hankali ta karasa ta zauna daf da Hajia, Hajiar kuwa ta kama hannayenta tana kallon fuskarta ta kai hannunta wajen fuskar Tata ta ce" meye wannan idon ya yi jajaja ko baki yi barci bane?" MALEEK ya sake duban Hajia da kyau ya kalli RAUDA itama, sai ya mike yana tsintar dan fruits din tunda da wahala in ya samu abinci kafin ya fita yau kasa kasa ya furta" To ai shikenan Ni na wuce tunda ba'a bukatar shedu" RAUDA kuwa a sanyaye ta ce" na yi Hajia, girki dai nake , daga kicin ne na taho da aka ce ana kira, shi yasa ban zo da wuri ba" Hajia ta kalli Mah tana kama baki ta ce" 😍😍😍😍😍😍😍😍 Azl 60 *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo Hajia ta kalli Mah tana kama baki ta ce" Lah, ki ga y'ar nan da neman fitina? waye ya aike ki? haba nima fa safiyar shiga kicin din na maki, haba dai, sai kace ba amarya ba, kin ga kina ji?, ki kula kin ji? a zamanku ki kiyaye haki, ki kuma girmama y'ar uwarki, ita abokiyar zama tana da dadi domin a rayuwa idan har ka zauna lafiya da ita zaka fi kowa jin dadin hakan, saboda yau da gobe ta fi karfin wasa, idan kunna jituwa ko abin dadi ya samu ko na wuya sai kun fara kama junna kafin mu ji, bana son jin wata fitinar kin ji ko?" RAUDA ta gyada kai tana sada kai, ita kuwa Amnah sai kawai ta mike ta fice , dan ba zata iya gannin wannan abin bakin cikin da rainin hankalin ba, ko a me Hajia ta dauketa? lalle Hajia ta gama daukarta a wata shashasha, wato ita za'a nunawa an fi son wancen banzar tsintaciyar magen a kanta ko? ba damuwa su zuba su gani! Gannin ya bi ta baya ya tabatar mata bangarensu ya koma, dan haka da gagawa ta je ta karasa ta shiga ta nufi Part dinsa Tunda ta shigo ta ringa bin yannayin tsarin wajen da kallo masha ALLAH wajen ya kawatu fiye da tunanin bawa, haka kuma bedroom biyu ne da shi su kuwa sauran part din daidaya ne da dan madaidaicin falo bayan falon nan baba sai dayan part din da tsarinra ya yi ginnin dakunnan a jere wa'inda ke nuni da na yara ne Tunda aka bude aka shigo ya dakata da bale botur din wandonsa yana kallon falon gannin shiru sai kawai ya bale din ya dauki abin wanka ya shige ya rufe, ya san da an shigo, abinda ya barawa ransa shine ko waye ya shigo cikin su biyu ne, shi yasa ya shige wankan nan, saboda zaman fada yau dole zai yi Ya jima sosai a bayin, ya fito yana tsane ruwan jikinsa , a kugunsa da tawul daure mai fadi, sai karamin da yake goge jikinsa da shi ya nufo falon part dinsa ya bude ya fito yana sauke dubansa a kanta Itama mikewa ta yi tsaye da sauri ganninsa a haka, gaba daya ta gaza dauke idannuwanta a kansa saboda irin yadda ya yi freshh da abin ruwan wankan dake diga a jikinsa "Amnah, lafiya?" Ya tambayeta da kula yana karasowa inda take tsaye gabanta ya yanke ya fadi gannin ya nufo ta kai tsaye ba wani tsaye tsaye Yana zuwa da kanshin sabulun wankansa da irin hucin da jikinsa ke fitarwa da tarin kwarjinin da Allah ya masa ya dan dago fuskarta yana kallo kasa kasa sosai ya furta" Aush, sorry wifey, zai huce, idan bai huce ba zan sa a kai ki clinik lafiya ki ga docter Papalo na tabata yana da maganin ciwon ki....." Babar duniyar da Amnah ta shiga ta farin ciki gannin wannan kulawa harda ambatonta da matarsa ce ta katse lokaci daya daga tsayen d atake wata irin mahaukaciyar juwa da tashin hankali suka sakata yin baya ta maku a kasa jikin kafet din wajen idannuwanta a waje ta dago a firgice tana kallonsa tana kokonta abinda ya faɗa Da yannayin ya damu sosai da yannayinta ya ce" Subahanallah, Kai, meye haka? kar ki ji rauni mana yi a hankali........." Ya yi alamun zai duka ya kamata, ita kuwa ta yi saurin dafa cafet din ta mike kirjinta na dokawar da ta wuce misali idannuwanta na neman rufewa ta juya da sauri tana fadin" Am, eem, ina zuwa, bari in je na dawo" Ta fice da mugun sauri, shi kuwa ya mike ya bi bayanta hankali kwonce har falo sannan ya tsaya yana kallon shigewarta dakinta da rufo kofar da ta yi jikinta sai rawa yake yi , hakan ya sa ya sauke murmushi ya juyo hankali kwonce idannuwansa suka sauka cikin na RAUDA dake tsaye da cokali a hannunta , ko me zata yi da shi oho, jikinta dauke da wata mahaukaciyar doguwar riga ruwan maroon mai laushi, gashin kanta daure, a kanta ko dankwali babu tana gaban table din jera abinci ta ga wannan ikon Allah Da farko murmushin ya dauke dif, dan umarnin da ya samu daga zuciyarsa kennan cewar kar RAUDA ta yi wani tunani a kan lamarin, sai kuma ya kwato yancin girmansa ta hanyar dawo da murmushin saman lebensa ya wani motsa kugunsa sannan ya nufo inda take tsaye da cokalin nan a hannunta tana kallonsa Kai ta sada da sauri ta ci gaba da aikinta ta hanyar barin wajen zuciyarta cike da kunyar yannayinsa, ko dazun sakin bakin da ta yi ta ga ya fito da wani zani a kugu yana bale bale Tu sunna da wani bamakatarai ya bi wancen abar ne, bayan wannan ina ita ina sake kallon mutumen nan? sam ba kunya a lamarinsa "Meye zaki wani saka mana ido Ni da matata?" ya fada yana yafa karamin tawul din a gefen kafadarsa turus ta tsaya daga abinda ta yi niya ta juyo tana kallon kasa wajen yatsun kaffafuwansa a hankali ta furta" Ban san kunne ba, da ban bi da kallo ba" Gira ya hade yana fadin" Ki dago ki kalleni ido cikin ido mana, kina wani abu kamar wace ke tsoron mutane?" Baki ta turo tana sake juyar da kanta ta ce" To ka saka abinda ya dace mana, Ni a haka ba zan iya ba gaskiya" ta karashe tana idasa ajiye kwanon da ta dauka ta cenzawa waje sannan ta ci gaba da gyaran table din , dan kuwa girki suka sha ita da masu aikin bangaren , shine ta shiga gyara wajen dan ita a rayuwa tana da sha'awar girki ko dan ta ci ta more da bakinta Dan tsai ya yi na alamun mamakin furucinta, ya sake kallonta ya ga da gaske tana kiyaye kallonsa, hakan sai ya bashi mamaki ainun, ama kuma bai tsaya jan abin ba ya juya hankali kwonce ya nufi Part dinsa A hankali ta tsayar da dubanta waje daya tana jin wani radadin na ratsa mata kirji na abinda ta gani, sai kuma ta kora ta ci gaba da aikinta , bata son shigewa cen ita kadai, ta tabata gajiya zata yi da zaman, bata saba ba ko farko zama waje daya kuma sai Allah ya hadata da Mah itama mutun mai son aiki da tsafta, shi yasa basa zama sam koda yaushe cikin aikace aikacen su suke kala kala, shi yasa yau dinma ta fitowarta dan bata ga dalilin da zai sa ta nade a gado ba A lokacin da yake fesa turare ya dakatar da sauri kansa na sarawa sakamakon tinowa da ya yi a cikin mutanen dake masa girki harda kuku biyu maza Ajiye turaren ya yi ya fito idannuwansa na neman rufewa ya dawo inda ta zauna tana zuba abincinta ya sake bin shigarta da kallo ya ce " Ke da wa kuka yi girkin nan?" RAUDA ta kalli fuskarsa jin amon muryarsa kamar ranar da yake mata fadan nan, dan haka ta bashi amsa tana fadin" Ni da masu aiki" Hannunsa ya kai wajen goshinsa ya shiga murzawa da dan karfi sai kuma ya juya da sauri ya nufi hanyar nan ta baya da suka shigo shi da ita jiya ya dadana wasu numbobi ya bude ya fice Mikewa ta yi tsaye da sauri tana kallon kofar, gannin an rufo ya sa ta yi kasakai tana tunanin mutumen nan kamar wanda yake tare da almatsutsai masu saka shi shiga halin fushi da sauka a lokaci daya? kai ita kam ta fi kowa shiga wani hali a rayuwa gaskiya YUSUF na fita Taj ya karaso da gudu ya kawo gaisuwar da ya saba kawo masa kansa a kasa YUSUF ya rintse idannuwansa dan ba zai so jin amsar tambayar da ta zama wajibi ya yi ba, sai dai dole zai yi tambayar nan , dan haka ya ce" Masu dafa abincin nan maza tare suka dafa da RAUDA?" Kai Taj ya sake sadawa a hankali ya girgiza kansa ya ce" A'a sir, tunda chef din kicin din ta sanar min Hajia ta fito tana kicin na suka bar wajen lambu ina fatan ban yi laifi Allah ya kara maka lafiya" idannuwansa ya lumshe yana fitar da huci mai sanyi daga zuciyarsa, ya jima a tsayen nan kafin ya ce" Ka cire su a harkar kicin tunda tana son shiga,nd......" ya dan dakatar yana bin manyan talo talon dake yawo da kallo ya ce" Nd ko da wasa, kar wani ya shigo inda za'a iya haduwa da ita........Doka ce" Da sauri Taj ya amsa yana sake dukawa, shi kuwa ya juya ya nufi dakin da suke rufe masu laifi kirjinsa na masa zafi da wani tunani da ya yi a kan maganar da ake cewa idan ka bi ta wani sai an bi takan nan? ' innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, ya Allah ka yafe min abinda na ringa aikatawa, ya Ubangiji ka yafe min kurakuraina kar ka kamani da RAUDA.......' shine abinda yake ayanawa har ya kama karfen da Habu dan daudu ke ciki ya yi tsamo tsamo kamar kazar da aka saka cikin ruwan zafi A lokacin da AMNAH ta shige dakinta direct bayi ta nufa ta haye saman wc cikinta na kurdawa tamkar zata zubar da hanjin cikinta hankali take hannayenta saman kanta Tuni ta cire abayar nan dake jikinta ta Yar a nan ta saka hannayenta tana sake sosa kanta dan sai ta ji kamar tafia ake yi mata a cikin kan nata *Clinik lafiya, docter Papalo* kunnayenta suka jiyo daga bakin MALEEK? wannan wani irin tashin hankali ne? dama ya san Papalo? , Da karfi ta ja ruwa ya kora abinda ta aikata ta janyo pampon nan ta wanke jikinta ko sabulu mantawa ta yi da sakawa tsabar tashin hankali ta kuma fitowa dakinta ta duka ta warto wayarta tana dane dane hankali gaba daya yana daf da barin jikinta, domin ya zamto mijinta ya san rayuwar da ta yi da Papalo shine abinda ba zata taba so ya faru ba a rayuwa, dan kuwa da wahala idan har ya san haka ya iya zama da ita, ita kuwa in har akace zata bar daular nan komai na iya faruwa da ita, ta riga ta shigo rayuwar nan bata tunanin akoy wata bak'ar kadarar da zata fitar da ita, ko mecece, shi yasa ta kudurta aniyar a kwana kusa sai ta san yadda ta yi da yarinyar cen, sai ga wata fitinar na son bilo mata? Ringin take yi ama ba'a dagawa sai da ta yi ya kai sau biyar sannan aka daga kuma aka yi shiru aka ki yin magana har sai da ta ce allo sau uku sannan aka amsata da murya kasa kasa mutumen ya ce" Lafiya kike kirana?" Itama da yannayin a tsorace take ta ce" Kai zan tambaya lafiya na ji sunnanka a bakin MALEEK? ya sanka ne dama?" A zaune yake, sai da ta sa ya mike tsaye yana fadin" Ni? ya san Ni? a ina? a'a fa, wani irin sanina?" Amnah ta ja wani irin numfashi mai zafi tana fadin" Wani irin bai sanka ba, bayan yanzu yace min idan ban warke ba zai sa a kaini wajen ka ya san kana da maganin ciwona?" Shima sai ya samu kansa da shiga tashin hankali, a rude ya ce" Wani ciwon? kina nufin tun aikin da muka maki wata da watanni baki warke bane shine kika kama sunnana a gaban mijinki?, ba mun yi da wajewa ba mun gama neman junna mun gama nunawa mun san junna ko a lahira ba?, a kan mi zaki kama sunnana a gaban mijinki Amnah? kin san da yana iya lalata min dukkan abinda na tara ko? kin san da yana iya sakani a prison din da za'a manta da na taba rayuwa a duniya ko?, inace tarayar mu ban taba tirsasaki ba ko? shine zaki watsa min kasa a ido ki tona Ni a wajensa?" Itama muryarta a daukake fiye da tasa ta ce" Kai dan Allah ka rufe min baki ka bar ambaton abubuwan nan kuma ka daina kama sunnana kai tsaye kar wani ya gane wace Amnar ake nufi, an gaya maka banda hankali ne da zan yi maganar nan da wani ma bale mijina?, Ni yanzu na ji sunnanka a bakinsa bayan a nan palas muna da asibiti baba wace ta dame clinik dinka inma maganar asibitin ce yake, kuma kai likitan mata ne me ya haɗa fatata da kai?, a dole zan kirayeka dan in san abinda nake ciki, in haukanka, karamin haukanka ya sa ka bude sirrin abinda yake faruwa Ni da kai walahi sai na yi ajalinla, kuma kaima ka san ba Ni kadai ce zan shiga uku ba!" Shima ransa ne ya ji ya ɓaci, ya ce" Kin ga, ina gannin ba Ni kadai ne zan shiga ukun ba tabas, harda mahaifiyarki walahi, kuma maganar ki yi ajalina karya kike baki isa ba na rantse, ke dai zaki cire sunnana a ciki dan kuwa kin san in na budi baki sai na fada cewar da kika zo wajena neman maganin infection dinki da kika kwaso a wani wajen bayan na yi treatment din ki kin warke kika ci gaba da zuwa wajen nawa, ke ce kika fara nemana, kuma ana gobe aurenki ba Ni nace ki kwonta da Ni ba, ke ce kika kwonta da Ni daga baya na maki aikin nan ai ba Ni na kawo kaina ba , sannan mahaifiyar ki itace ke........." Dif ta kashe kiran tana zarro idannuwa cikinta na sake murdawa, a dole ta shiga kiran layin mahaifiyarta dan kar fargaba ta kasheta ita kadai a daki, gaba daya tsoro ya gama mamaye mata zuciya da tashin hankali A irin wannan lokacin kuwa mahaifiyar Tata sunna zaune a falon gidansu ita da abokin mahaifinta da mahaifin nata sunna maganar abinda yake faruwar nan, su duka burinsu su gane ya ji abinda banzar jarababiyar tsohuwar nan ta fada ne ko bai gane komai ba?, hakan ya sa wayar ke ta ringin bata gani ba kasancewar a silent take matarsa uwar gida ce ta shigo dauke da jus da kayan kari ta ajiye, kanta kasa ta gaishe da su ta juya ta fice, a zuciyarta tana adu'ar Allah ya sa su ci abincin kamar yadda akace a saka adu'ar nan WARAFA'ANA'U MAKANAN ALIYA da aka rubuta dubu tara da casa'in da tara, akace idan da hali duk wanda ake tunanin da saka hannunsa a lamarin ya sha, to kuwa in sha Allah za'a fara gannin haske a maganar asiri, domin adu'ar nan waraka ce sosai bale a harkar samu, shi yasa da sakon ya zo yau daga fada ita kuma ta maida hankali ta yi girkin nan da jus ta kawo tana ta adu'ar Allah ya sa a dace Hankali kwonce Hajiar AMNAH ta mike ta zubawa kanta abincin ta koma da abinta ta zauna, shima mahaifinta da kansa ya zuba nasa ya zauna hakama abokinsa da ya bararaje tamkar gidansa ya zuba ya fara cika jus din ya koma ya zauna ya shiga shan jus din sannan ya dora girkin kusan kowane ya sha jus din nan, sai dai wani ikon Allah sun a sha ciwon kai ya saukar masu gaba dayansu gannin da gaske ciwon kan yake ya sa mahaifin Amnah mikewa, dama jikinsa du wani iri yau din, tun dazu da Hajia ta fara fadan nan jikinsa ya yi wani irin sanyi, ya mike ya nufi dakinsa yana fadin" 😍😍😍 *MAGANIN KARA KIBA 3IN1* *Ina meneman kiba ido rufe Kuma tanason maganine ingantacce Wanda baida illah kokadan to tazo gadama tasamu yar uwa indai kibace da gyaran nono dakara hips toga Mganinmu nan 3in1 cikin kwana 7 kacal👌🏻 zakiga yadda Zaki fara murmurewa insha Allah mungwada mungani munbayar angwada munsayar angode insha Allah kawata Zaki godemin da 3500 dinki kinhuta da gorin rashin kiba munan cikin Gombe Kuma munatura kaya ko ina kedai tuntumebi ta Whatsapp ko kikirani Kai tsaye ta 08030861857 sai kunzo🥰* *MAGANIN HIPS* *Wannan Maganin anyisane tamasu neman hips sunsha wannan sunsha wannan to gatamunan insha Allah guarantee nakebaki hajiya inada yakini akanta matsala indai tarashin hips ne to anwuce gun 3500 kacal kinhuta kijuya kiwarwasa kisaka kayan gayu kijuyawa Oga yayikallo kawata har yanga saikinmasa ninafadamiki wannan nemeni kisamu naki 08030861857* *MAGANIN NONO* *Itama akwaita me inganci kamarta 3in1 data hips wasu suna korafi nifa nono kawai nakeso yaciko yayi bulbul gwanin sha'awa yadda Oga zaiyaba nasa breast cup suzauna das Amman abun yacitura Nasha Nasha magungunan Amman haryau ba chanji to ganamu Nan yakine ne Dani akansa ba Dan kadanba alhamdullahi duk Wanda yasaya saidai godiyace tsakaninmu kema zokigwada Kuma kigodemin location Gombe 08030861857* 😍😍 Mahaifin Amnah ya kusa shiga dakinsa yana rike kofar dakin ya ce" Idan ka tashi tafia, ka fadawa Ilu mai shagunna ya saki shagunnan nan Please" Daga haka ya shige dakinsa yana jin kansa sai sarawa yake yi Furucin ilu mai shago ya saka abokinsa binsa da kallo sannan ya kalli Hajia da ita dinma ta kalle shi da sauri, Dukda yannayin da take ji a jikinta bai hannata fadin" Ilu mai shago kuma?" Shima abokin nasa yana kallonta ya ce" Lafiyarsa kalau kuwa? a shekara goma ma ya yi maganar dukiyarsa? idan akace da su Ilu su tashi ace masu a kan wani dalili bayan sunna biyan kudi a kan lokaci?, ki binciki mijin ki fa, wani iri nake ganninsa" Dan shiru ta yi tana kallonsa, sai kuma ta mike ta nufi ciki wajen Elhaji a ranta tana tuna maganar wanda ya bata rantsatsen aikin nan, bata tunanin kuwa gawa na dawowa duniya bale har ta ciro abinda yake bakinta a dinke wanda aka dinta mata saboda aikinsa, kawai tana kyautata zaton dawowa ne abin ya dan masa sama sama, bayanshi ba dai ace wai ya dawo hayacinsa ba Tana shiga ta same shi yana ta barci, sai zufa yake yi, dan haka ta ficewarta ta barshi tana dan fitar da tsakin zai bata mata lokaci a kan shirmensa ____________________________________ Taj ne ya zo inda yake tsaye tun dazu ya kurawa habu dan daudu ido, wanda tunda ya tsaya din nan shi kuwa ya duka hannayensa a hade yana duban kasa sai rizgar kuka yake yi wanda shi da kansa bai san ko na meye ba Da girmamawa Taj ya ce" An saka sakon a hannun uwar gidan nasa, kuma an tabatar da ta tabatar da sun sha" Ya jima kafin ya iya budar bakinsa yana duban Taj ya ce" Thank you, Please kar a daina har sai Allah ya tabatar mana da maganin da muke nema , sannan a sake kaima babar abinci" Taj ya amsa yana risinawa har ya juya YUSUF ya yi kiransa dawowa ya yi ya sake dukawa A hankali ya ce" Taj, sirina ya zama siri a gareka" Taj ya karra sada kai a hankali shima ya ce" Mudin raina MALEEK" Daga haka ya salame shi, ya ciro ky din wajen da Habu yake ya bude ya shiga ya rufe daga ciki ya nemi waje ya zauna yana kallon Habu Ajiyar zuciya ya sauke, gaba daya karfin jikinsa ya bar jikin nasa ne tunda tunanin nan ya shiga zuciyarsa A tausashe yana kallonsa ya ce" Zo nan ka zauna" Habu ya kalli inda ya nuna masa,, ya karra sada kai a raunane ya ce" Ranka ya dade, dan girman Allah ka gafarta min, Ni ban san laifina ba sai ganina na yi a nan, ka yi hakuri ranka ya dade" YUSUF ya sake dubansa a tausashen ya ce" To Ni na zo ne?" Da sauri ya girgiza kansa ya mike ya je ya duka kusan kaffafuwan YUSUF kansa a kasa Yusuf ya sauke ajiyar zuciya yana dubansa ya ce" Ka ga, ka daina sada kan nan, bashi da wani anfani, dan ban haliceka ba, wanda ya haliceka na jiranka, ruwan ka ka shiryu ko ka je masa a haka, abinda nake so da kai tambaya gareni , na san kai aminin matata da mahaifiyarta ne, tunda na ganka da idona ranar da muka gaisa a falona" A haukace Habu ya dago yana dora hannayensa saman kansa, jikinsa na karra daukan rawa YUSUF ya dan sauke ajiyar zuciya shima yana kallon nasa ya ce" Ka daina abin nan mana, kai fa namiji ne......" Sai kuma ya dan yi murmushi a saman lebensa ya ce" Au ashe ba haka ba, ka ga, ina so ka fada min sirrin asirin da ya saka Elhaji zama kurma kuma makaho a kan abinda ke tafe a gidansa" Wannan karron kam, ya san tasa ta kare,dan kukan na dazu ba ihu na yanzun harda ihu yana sake dora hannayensa saman kansa ya ce" Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une na shiga uku, Ranka ya dade ka ga daga Allah ba wani? Ni nan dan aike ne kuma yaro a wajen Hajia, walahi du abinda za'a aikata Ni dan rakiya ne dan na samu dan abincin ci a bakina bayan wannan babu wani abin, dan Allah ka min rai ka yafe min shiga gidanka da na yi da kuma zamowa tare da matarka, idan na fita daga nan ko sunnanta ba zan kuma kamawa ba" YUSUF ya yi shiru, sai kuma ya girgiza kansa kawai ya mike yana ciro ky din aljihunsa ya nufi kofar A rikice Habu ya rarafo yana fadin" Innalilahi ranka ya dade dan girman Allah kar ka barni a nan, ka ceci rayuwa.........." "Kai ja baya dan ubanka kar na datse maka hannaye!" Taj ya fada da hargagin da ya sa Habu saurin yin baya fitsari na sake kubce masa a wandonsa, dan a zamansa a wajen nan fitsarin da ya yi a wando ya fi a irga, ranar da suka likira shi ya saki fitsari Taj cewa ya yi ashe yanada alkalami a jikinsa yake daura zani Murya na rawa, jikinsa kaf na rawa, kana ganninsa ka san ya gama fita a hayacinsa ya ce" Ranka ya dade zan fada dan Allah kar ka barni da su, walahi kasheni zasu yi, ranka ya dade ko muryarsu tsoro nake yi, dan Allah kar ka barni da su, walahi a wata gawar wata budurwa da ta rasu a anguwar su Hajiar aka dinke layar da aka basu, sunne suka yi wankan gawar Hajiar ce ta saka da kanta dan aminiyar Uwar yarinyar ce, ita ta fada min cewar daga baya ta biya aka bi gawar aka dinke mata bakin dan kar layar ta fadi, ranka ya dade na san gidan su yarinyar, ama ban san inda kabarinta yake ba, dan Allah a sakeni zan nuna" Kansa banda sarawa babu abinda yake yi, a hankali ya lumshe idannuwansa ya bude din ya fice yana jin ihun Habu ya nufi bangaren Mah idannuwansa na neman rufewa Da kyar ya iya sada kansa da dakin Mah, a lokacin tana zaune tana shan maganinta ta dago da sauri tana kallonsa har ya karaso Maimakun ta ga ya haye gadon ya zauna daf da ita sai ta ga ya zauna a kasa sannan ya dora kansa a saman kaffafuwanta "Kai lafiya?" Mah ta fada da sauri tana dubansa Sai dai bai dago kansa ba daga irin yadda ya dora kan nasa a cinyar nata Da sauri ta saka hannayenta ya dago kansa sakamakon jikar da ta ji cinyarta ta yi , jika mai dumi , jika mai nuni da hawaye ke sauka a kan cinyarta na Yusuf Da sauri ta sauko ita dinma daga saman gadon tana talabo fuskarsa ,, muryarta na rawa ta ce" Menene? subahanallah me yake faruwa? ina Bah dinka? ina Hajia? ina baby? ina Amnah ne? menene Ishak ne? ko Taj? menene YUSUF?" Da sauri ya mayar da kansa cikin tafukan hannayenta ya ja wani irin numfashi hawayenshi suka sauka sosai yana rike da hannayen nata gannin tana daf da sumewa dan shiga a halin kidima a dole ya budi bakinsa yana dubanta a hankali ya ce" Lafiyarsu kalau Mah" Mah na dubansa idannuwanta sun gama cikowa da kwallah ta ce" Mememenene to? kuka fa kake yi fa" Yusuf ya langwabar da kansa yana dubanta, a hankali ya ce" Mah, anya kuwa zan iya?" Mah ta sake rikicewa tana dubansa ta ce"Mene? meye ba zaka iya din ba? sarautar kake son ajiyewa?" Kai ya girgiza a sanyaye ya ce" Inama ace sarautar ce nake son ajiyewa, sai na ajiye dam na dauke ki mu gudu, kin ga abin nan ya fi karfin wannan Mah, walahi ya fi karfin wannan rigimar" Zuwa yanzu kam Mah ta gama rikicewa, da dan karfi ya ce" Kai, wai uban meye?, zaka fada min ko sai na fala maka mari?" Idannuwansa ya sada kirjinsa na dokawa, a hankali ya ce" Idan fa abinnan ya bi Ni har yayana?, Mah idan rashin jin da na ringa aikatawa na biye biyen mata ya bi Ni har yayana? yaya zan yi?" Mah ta yi dif gabanta na faduwa tana kallonsa, ta kasa furta koda kalma daya ce A hankali ya sake fadin" Kin ga, tun ba'aje ko'ina ba, matata , uwar gidana, bata jin magana, ta yiwu fiye da rashin jin da na aikata a da, dan abubuwan da nake gani a hankali da wa'inda na gani sunna karra rikita min lissafi, a yanzu Ban san ta ina zan fara ba, dan kuwa tsoro ya gama kashe min duk wani kuzarina da yunkurin daga nake iya yi" "Rashin jin, na menene? kana nufin bayan da igiyar aurenka tana kara ci gaba da rashin ji? ko menene girman tashin hankalin da kake fadi dan Allah?" Mah ta fada a sanyaye tana dubansa, zuciyarta kuwa cike da tsoron amsarsa Ajiyar zuciya ya sake saukewa yana dubanta ya ce" A yanzu, ai bata fita Bama bale ta aikata, koda ace zata iya ci gaban bayan auren, wanda ya shigo da sunnanta kuwa dan daudu ne anya zata iya zubar da kanta har haka?" Gaba daya Mah sai 5a dawo bata gane yarensa, kallonsa take yi ta kasa gane komai, sai take gannin kamar wanda yake yi mata wata maganar ta wasu daban, dan haka a tausashe ta ce" YUSUF, dan Allah ka min bayanin yadda zan gane ko zan iya taimaka maka da addu'a, sannan na yi maka nasiha? domin na sani ko menene ba zai gagari yafiyar ubangiji ba in sha Allah " "Mah, mahaifinta fa ba shi ya haifeta ba, kuma ana jibi aurenmu ta aikata zina da likitan da ya yi mata aiki ya dinketa bisa jagorancin mahaifiyarta, Mah kin ga dai mahaifiyar Amnah ko ta gama kuncen kaina da na ji cewar wannan hali da mahaifinta ke ciki wai asiri ne kuma a gawar y'ar kawarta ta anguwa suka saka, to yanzu Ni gaba daya na gama rikicewa, inaga da wahala in Allah zai yafe min, tunda da ace mutumen kirki nake da wahala Allah ya hada hanyata da mutanen nan, Ni da kaina na daina yarda da kaina yanzun Mah....." Ya karashe yana rike hannayenta , ta yadda zafin tafin hannayensa ke ratsa nata da irin yadda bugun kirjinsa ke shiga kunnayenta kawai sun isa su tabatar mata tabas a mugun yannayi yake ciki A hankali ya dora da fadin" Na rasa ina zan kama, dan kuwa na san ba zan iya zama da ita ba Ni dai, wannan tashin hankali dake tare da ita ya fi karfina, ina bibiye da su ne a hankali tun daga ranar da Taj ya zo min da magana a kanta kan binciken da na sa ya yi, domin a ranar da aka kawo ta fa kanta ta kai cen bangaren tace min wai gata, sai na ji tsoron kar aje banda rashin kunyar akoy wani halin ko na tabuwar hankali ko makamancin haka dai, sai kawai abubuwan nan ke fitowa, Mah a sanadiyar asirin da mahaifiyarta ta yi , mahaifiyar Elhaji ke daka daka dan ta ci abinci a daya daga cikin kangonsa, matar nan tana ji tana gani, ba zata iya taimakawa wannan baiwar Allahn ba ko dan rabata da ta yi da d'anta, sai da muka ji ne aka kawo ta nan take zaune har mu ga abinda Allah zai yi, yanzu Mah wannan ai ba tsatson hada zuri'a da su bane ko? shi yasa nace kawai tunda malan ya tabatar min akoy aurena a kanta sakinta zan yi in komai ya daidaita" Mah ta jima tana innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, da kyar ta daidaita tunaninta ta kalle shi har ta iya sauke ajiyar zuciya tana sake dubansa ta kuma sada kanta sannan ta dago a tausashe ta ce" Ka saketa ka ce?, to kai kana tunanin kowa zai so hada zuri'ar da kai ne Yusuf?, kaima fa abin gudun mata da yawa ne in fada maka gaskiya, kuma a bayanan nan da ka yi inaga in dai ba ta san dukkan shiga da fitar mahaifiyarta ba laifinta daya ne irin sana'arka wace idan Allah ya sa ta shiryu ne ta dalilinka sai ka ga ka kilaceta har Allah ya sa ta zama abar kwatance gobe, domin da yawa a rayuwa ai ana aikata laifi idan an tuba ka ga an yi kyakkyawan tuba an shiryu har an zama abin kwatance, in ba wannan ba YUSUF ai da an halaka sosai a duniya, dan kuwa da yawa sun ci gaba da aikatawa kansu tsaye tunda dai tubar ba wani anfani ko Yusuf? ko dan Amnah mace ce ta aikata irin halayanka zai zamo abinda za'a yi riko da shi a kasa yafe mata har a bata second chance din da zata rayu itama rayuwa mai kyau? ko so kake ka nuna min cewa lalle kai din jinnin Hajia ne da basa yafe irin wannan?" Da sauri ya kalli Mah, hankalinsa na neman tashi ya ce" Mah, a'a fa, ya Salam ba haka nake nufi ba fa,Mah ki duba ki ga halayanta, ki kuma dubi iyayenta, inace addini ne ya koyar da mu samawa yayanmu iyaye na gari dan gobe su yi alfahari da mu ba? halayarta nake ta dubawa, ina ta yi mata uzuri , Mah sai dai bata da wasu qualities da zan so, kin san da na san bata son ki, haka bata son Hajia, kin san da na san Hajiar su Salima ce aminiyarta wajen zuwa shawararta, idan fa aka wayi gari abinda ya kasance da mahaifinta ya kasance da Ni na yi yaya? Mah bayan ku da kuke a wuyana garina ke wuyana, idan na zama sai yadda mace mai son kanta ta yi da ki ai na bani na lalace ko?" Mah ta sake lumshe idannuwanta, kwarai dukkan abinda yake fada gaskiyar kennan, sai dai tana so ne ya zamo ya yi sadaukarwa ya kuma bata dama saboda rayuwa, da kuma fatan Allah ya dubi aiyukansa na kirki ya yafe masa na banza, dan haka tana dubansa ta ce" Ka ga, a duniya babu abinda mutane basa yi saboda dukiya da mulki, kuma a abinda ka fada sai an zauna za'a gane in ƴaƴanta sunna tare da ita kuma in sun san abinda yake faruwa da su, bayan wannan Ni uwa ce, kuma wace na ga rayuwa kala kala, ba zan tashi tashi guda in hade kowa da kowa a laifi ba, kwarai iyayenta sunne tushen tarbiyarta, ama kuma Allah mai shiryar da bayinsa ne, idan ita din da rabon hakan sai a bata dama, haka din baban jihadi ne, idan kuwa ta yi nisa a tafiyar bata jin kira sai a salhance mata ta hanya mai sauki ta yadda Allah zai yi duba da halayan da aka aikata dominsa masu kyau ya yi yafiyar wa'inda aka aikata marar kyan, ka fahimta?" Kai ya gyada yana duban Mah Mah ta dora da fadin" a duniya bawan da zai ringa aikata sabo yana sane ya kasa tuba ne abin tausayi, da kuma bawa mai yin tuban muzuru, bayan wannan duk wani wanda ya aikata laifi ya koma ga Ubangijinsa to ya ci gaba da astagafari in sha Allah Allah zai yafe masa......... ka yi rashin ji YUSUF, ama ka daina right?" YUSUF ya gyada kansa yana kallonta da sauri Mah ta yi murmushi ta ce" To ka bar sake saken munanan tunanin da suke iya tsayar maka da numfashi, idan ka haihun ka saka albarka ka kai makaranta ka yi nasiha ka yi hakuri, dukkan sauran abinda Allah ya yi mai kyau ne ka fahimta?" Yusuf Ya ce" Eh" Mah ta ci gaba da fadin" Dukkan wani wanda zai zageka da shi kuwa ka saka masa ido ko wanene, domin farkonsa ya sani bai san karshensa ba, idan ya zamo mai isgili sai Allah ya jarabce shi da farkon ka, a lokacin zai gane cewar jarabta ce ta Ubangiji, ka ci gaba da taimakawa baiwar Allahn nan, ka kuma jajirce wajen kwato mata yancinta, Amnah ka yi hakuri ka gyara zamanku, kar ka sauta sai idan ya zama dole, kar ka wulakantata saboda abinda ta aikata ko iyayenta suka aikata, idan ka tashi yi mata shara'a ka yi mata cikin sirri saboda iyalinka ce, ko yau ka rabu da ita ta taba zama matarka, maganar bata son mu kuwa ka bata lokaci in da rabon ta so mu fine, idan bata son mu YUSUF normal ne ba wani abu tsakaninmu da ita mu, domin iyayenta muke daga wannan ba wani abin, YUSUF zaka iya yi min haka kuwa?........." 🥹🥹🥹🥹 Allah ka gafartawa iyayenmu Azl 62 *MAGANIN KARA KIBA 3IN1* *Ina meneman kiba ido rufe Kuma tanason maganine ingantacce Wanda baida illah kokadan to tazo gadama tasamu yar uwa indai kibace da gyaran nono dakara hips toga Mganinmu nan 3in1 cikin kwana 7 kacal👌🏻 zakiga yadda Zaki fara murmurewa insha Allah mungwada mungani munbayar angwada munsayar angode insha Allah kawata Zaki godemin da 3500 dinki kinhuta da gorin rashin kiba munan cikin Gombe Kuma munatura kaya ko ina kedai tuntumebi ta Whatsapp ko kikirani Kai tsaye ta 08030861857 sai kunzo🥰* *MAGANIN HIPS* *Wannan Maganin anyisane tamasu neman hips sunsha wannan sunsha wannan to gatamunan insha Allah guarantee nakebaki hajiya inada yakini akanta matsala indai tarashin hips ne to anwuce gun 3500 kacal kinhuta kijuya kiwarwasa kisaka kayan gayu kijuyawa Oga yayikallo kawata har yanga saikinmasa ninafadamiki wannan nemeni kisamu naki 08030861857* *MAGANIN NONO* *Itama akwaita me inganci kamarta 3in1 data hips wasu suna korafi nifa nono kawai nakeso yaciko yayi bulbul gwanin sha'awa yadda Oga zaiyaba nasa breast cup suzauna das Amman abun yacitura Nasha Nasha magungunan Amman haryau ba chanji to ganamu Nan yakine ne Dani akansa ba Dan kadanba alhamdullahi duk Wanda yasaya saidai godiyace tsakaninmu kema zokigwada Kuma kigodemin location Gombe 08030861857* Muryarsa a matukar sanyaye yana kallon Mah, zuciyarsa cike da sake saken abinda Mah ke son a yi wanda yana kyautata zaton da wahala ya tabatu ya amsa mata a tausashe kamar haka" In sha Allah, Mah zan yi, in dai na tabatarwa kaina cewar a abubuwan nan da na zayana din, laifin Amnah abinda ta yi a baya ne, kuma baya da niyar yin wani zan dubeta, koda kuwa na taba zmbatar kalmar haramtawa a gareta a kankin kaina zan sake neman malamai su daidaita lamarina da ita, Allah ya sa hakan ya zamo silar gogewar zunubaina " Mah ta sauke ajiyar zuciya, zuciyarta cike da rauni ta amsa shi da Amen Zaman nasu kasa daukan lokaci ya yi, ita da kanta burinta ya tashi ya fita dan tuni ta yiwa Bah msg din tana son ganninsa yanzu, burinta ya tafi ta iya daidaita nutsuwarta, shi dinma kuma gaba daya ya sake shiga a wani yannayin daban, mai kara hargitsa masa tunani, a dole ya mike yana murmushin dole ya mata salama ya kuma komawa bangarensa dan baya tunanin a yanzun kuma zai iya zuwa wani wajen, ko a bangaren nasa ya san ba zai iya samun wata nutsuwa ba sai wani firgicin da tashin hankalin Yana tafiya Mah ta cire hijabinta ta shiga yamutsa gashin kanta hankalinta tashe idannuwanta suka kama zubar da hawaye Innalilahi, da ace za'a shiga zuciyarta da an ga tarin tausayin yaronta dake son halakata, sai dai duk abinda take ji in sha Allah zata jajirce ya gabatar da abinda zai tsira gobe kiyama, tunaninta a wajen da ya fi tsayawa shine *SHIN YUSUF NA GIRBAR ABINDA SU SUKA SHUKA NE, WATO YUSUF NA AMSAR HUKUNCIN ABINDA SUKA AIKATA NE HAR YA SA SHIMA YA DANDANA MASU ABINDA SUKA DANDANAWA IYAYENSU, HAR YANZU ALLAH YA NUNA MASU YA SHIRYU KO SHIMA YUSUF DIN ZAI HADU DA NASA HUKUNCIN DAGA WAJEN ALLAH????????* Tunaninta ne ya katse da zubar hawayenta sakamakon shigowar Bah alamunsa daga barci ya fito domin jalabiya ce a jikinsa, kuma yau yana ɓangaren Hajia ne, wato mahaifiyar Salima shi da kansa ya san kiran nan ba na dadi bane, domin idan baya bangaren Mah bata so ya zo dan gudun rigimar matansa da suka kasa girma idannuwansu a kan dan karamin abin da yake iya zama abin a ji kunya idan aka ji ya fito daga su suke jira su yi masa daukakawar da kowa zai ji a yi rikicin da bata so ace a yanzu dai , da girma ya gama kama su, suke aurar da y'aya sunna fada a kan abin da ita rabontama da shi an jima, shirme kawai sun kasa gane an riga an zama daya fiye da tunaninsu, su suke ha baba ha karami a kan lamarin nan, ita a yanzu ta lafiyarta ai ta fi komai gaskiya Kamar yadda ya zama abokin sirrinta, mutumen da idan abin ga yi kuka da burgima ya kama shi take yima, mutumen da koda abu bai shafe shi ba takan saka shi a ciki dan ta gama yarda cewa a nan gidan duniya shi din nan shine sirrinta kuma shine mai sauraronta ya bata shawarar da ta dace koda ba zata yi mata dadi ba, ya sa a yanzunma ta neme shi a fujajan suka zauna a kan abinda yake da ruwa da tsaki a ciki kamar yadda take da shi, ta shiga sanar masa abinda ya gigita shi fiye da tunaninta harma tsoro ya shiga kamata a lokacin da ta sanar masa abinda ta fadawa d'an su, kuma Sarkin garin su, cewa eh, dukkan abinda ta zayana din nan kuma a haka zai zauna da yarinyar harda fadin a ba yarinyar chance din da ya dace dan idan ta gari ce a zauna da ita, in kuwa ta dauko maganar da ake da tabbacin in dai ta samu hanya zata dauko din sai a bata salama cikin salama ko me? ransa ya ɓaci yana kallonta, duk irin hucin zafin da jikinta ke fitarwa yau kam ya kasa hakuri yana kallonta da kausasawar da bai taba yi mata ba ya ce" NA JI, kuma na fahimci dukan bayanan nan da kika fada, sai dai abinda nake son karra tabatarwa shi ne, YUSUF ya nufo ki, a yannayin gigitar da kika ce ya yi kuka, sai kika karra tabatar masa eh hakan da yake faruwa da dukiyarsa daidai din kennan kuma dole zai dauka?" Kallonsa take yi, gannin kamar ransa a wani iri ba yadda ta so ji ba ta ce" Eh abu YUSUF, haka na fa......." "Dan Allah zaki iya yin shiru na second biyu?" Ya fada a tsawacen da ya sa ta zabura tana kallonsa gabanta na faduwa Rai bace yana dubanta ya ce" Ke, kisa ake yi idan an yi shara'ar da Allah ya rubuto Allah ya yafe a yadda muke kyautata zato domin mu musulmai ne, ke Ameerah bulala kike so a masa ne? Sai na kai shi kotun musulunci a kwontar da shi da hannayena na masa, ko mu din zamu je mu sanar kafin a mana aure mun yi rashin jin da a yanzu rayuwar nan yannayin zamani da ya zama haka daidaikun samari da y'an matan ke tsalakewa suke nan kuwa su tuba su dawo su bi Allah, Allah ya dube su saboda dama d'an Adam Ajizi ne, kuma Allah yace da ace dan Adam zai rayu ba yin laifi ya tuba, da ya shafe duniyar ya zuba wasu, ko baki dan cewa ka yi laifinma ka daina babar daraja bace da zaki ringa rayuwa a matse, a takure, ki kuma takurawa yarona a kan haka har ki budi baki ke AMEERAH ki ce da YUSUF zai rayu da yarinyar nan?!" Ya karashe muryarsa a sama saman da ya saka Mah sake shiga a halin tsorata tana kallonsa A kausashe ya ci gaba da fadin" Inaga dan kin haife shi, yana karkarshin yi maki biyayya ne kika kasa yarda da darajarsa da kuma girman da Allah ya bashi, ina tunanin dan YUSUF bashi da wajen zuwa ya zubar da hawaye sai jikinki ne kike aiki da wannan damar a tunaninki so din ne kina karra daba masa wuka a zuciya, Ke Ameerah da yawa sarakan ne suke badalar kuma da matayen na kirki sun kilace, manyan masu koyar da tarbiyyar ke aikata badalar kuma sun kilace iyalansu, ban san me iyalansu ke aikawa a boyen ba, abinda na sani shine Allah gafurun rahim ne, ban ce d'ana bai yi laifi ba, d'ana ya yi laifi sosai, kuma na fi kyautata zaton dan na taba y'ar wani Allah ya jarabceni da d'ana mafi soyuwa a zuciyata ke wannan halaya marar dadi, yake fitinar kowa a da, kuma Allah ya amshi adu'ata har aka wayi gari YUSUF ya bar aikatawa ke kin san ba dan yana tsoron dan Adam ba ya daina dan na wannan tsarin a duniyarsa, dan yana tsoron Allah ya daina, kuma mun yarda da tubansa domin baya rayuwa dan ace ko a gani, shine zaki duban min yaro ko rikita shi?.......... AMEERAH!" Bah ya sake fada yana dafe kansa da hannayensa bibiyu ya sake dubanta idannuwansa sun gama yin ja, ya ce" Inaga Nine baki yafewa ba, da ace kin yafe min da baki min haka ba, Ameerah a me kika dauki sarauta?" Mah tana kallonsa hankalinta gaba daya a tashe ta ce" Bello, dan Allah ka kwontar da hankalinka mu yi magana, a ganina d'a ai duk na kowa ne, kuma yarinyar nan idan an bata dama an rungumeta ina ga ai aikin lada aka yi ko?" " Tabas baki san menene sarauta ba, kuma kallon nan da kike yiwa d'anki a bagas ya sa kike tunanin irin kowani mutun ne da yake iya daukan wannan rayuwar!" Bah ya sake katse Mah, sannan ya juyo ya fuskanceta ya ce" Ki yi hakuri da kiyayar da Hajia da ahalina suka nuna maki koda kuwa mu din nan mune ke dauke da gagarumin tabo na rashin ji a gidanmu, sai dai kuma sarauta gare mu!, ki yi hakuri da kika ga sun kasa yafe maki da wuri yadda ya kamata ba dan kin fi kowa laifi bane ya sa yadda lamarin ya zo mana ne, ki gane Nine na ja maki tsana da na kasa hakura da ke na kasa baki lafiya, na kasa barinki ki yi rayuwarki da wani, tunanin wanina na iya daukan ki bayan ke tawace, rayuwata ce ya sa na kasa baki damar ki rayu cikin farin ciki na saka maki kunci mai tsananin da har kika kasa gane Allah kika yiwa laifi ba uban wani ba da har za'a kasa dubanki a cikin al'umma bayan ke din mai kyakkyawan tuba ce, tunda kika yarda da abinda na saka ki kike kuka har zuwa yau, a haka na jajirce bayan na san in na aureki ba Ni ba sarauta, na yarda na auri abata dan na zabe ki a kan sarauta, kuma na san zaki zabe Ni a kan farin cikinki ......sai dai baki sani ba Ameerah, baki sani ba, an yarda an aura min ke ne dan an san iyayenki, Ameerah walahil azim sarki ya aura min ke ne dan an san tsatson da kika fito, kuma sarki ya fadawa Hajia ta taka a hankali, kar ta yarda ta yi abinda zai bata hutun rayuwa tsakaninsa da ita, ya yarda Kadara ce ta fada tsakanina da ke, domin mahaifinki malamin tarbiyya ne, mahaifiyarki jinnin dan sawani ce, kuma yan anguwa sun sheda tarbiyyar ki!, saboda wannan ne kika samu rayuwar nan da kike gannin ta fi ta kowa muzanta a duniya AMEERAH, me zaki iya cewa da tsatson da AMNAH ta fito da kuma tarbiyarta?!" ya ajiye maganar dan ya karra sanar mata a shirye yake da ya yi jayayya da ita wannan karron, duka wanda bai taba jin kansu ba zai ji sannan ya dora da fadin" Na ce, me zaki ce a kan tarbiyarta?, me zaki ce a kan mu'amalarta da talakawa?, inace nan na taya ki kashe maganar korar macen da ta yi mata salama dan tana waya a aiki a masarautar nan da ta yi, kuma a dan zaman da aka yi da Ni na abinda ya shafeta kafadata da tawa ke jere a saman kujera a lokacin da ke duwawunki ke kasa dukda kina da ciwon kafa saboda taki SARAKUWAR a saman kujerar!, kin ce an zo da dan daudu da magungunnan da d'an daudun ya kwashe wanda ke tabatar maki koda bata san waye ubanta ba ta san asiri ke tafe da mahaifin da take yiwa kallon uba a gareta hakan har yana birgeta dan kuwa gashi an kawo mata har gida ta kai katon dakinta na sunna , kuma mahaifiyarta ta kwana a nan din, Ameerah so kike yi sai an wayi gari YUSUF ya kore mu daga fada bisa umarnin matarsa zaki yanke jiki ki fadin min ko me?, ko so kike ki ce min ko a tarihi baki san cewa SARKI baya auren muguwar mata a sanin kansa, sai dai idan daga baya zata aikata masa da muguntar a cikin gidansa, rayuwa ta yau da gobe ta sa ta zama muguwar?..........., shine dan kin dauki SARKIN GARINKI abinda kike iya juyawa yadda kike so, da tunaninki zaki yi masa umarnin zama da macen da aka tabatar masa ga abokin shashancinta? kin san girman abin nan kuwa? ace namiji ya ga mutumen da matarsa ke shashanci da shi koda matar kiyayarsa ce kuma ace ya yi rayuwar aure, rayuwar da ba sirri tsakanin mata da miji ? haba Ameerah......." Bah ya karashe wannan karron muryarsa a tausashe, yana dubanta ya ce" Ina laifin ki ce a yiwa yarinyar nan sassauci, a yi lamarinta a siri sannan a dauki nauyin ta, a kilacewa a bata tarbiyya kuma a kaita dakin aure nesa da kasa a bata damar gina rayuwa in har ba hannunta a cikin dinke laya a bakin gawa? ama sai ki ce a rayu da ita a haka bayan ana magana ne ta uwar al'umma ba uwar jikokinki kadai ba, ana magana ne ta gimbiya ba wai matar YUSUF kadai ba, muna magana ne ta gidan tarbiyya ba y'ar aminin uba ba?" Ya karashe kirjinsa na daukan zafi yana rintse idannuwansa hadi da rike hannunta da karfin da ya sa itama dantse lebenta A kausashe ya ce" Ba zan iya ba, ba zan iya raka ki a wannan tafiyar ba, idan kuma kika ja zan ja, dan ba zai ce min komai na kai kararki a kan wannan maganar ba, AMEERAH a kan maganar nan zan ja da duk wanda yace zai ja da Ni, kuma ki yi hakuri tunda kika sanar min dole a gaggauta neman iyayen marigariyiyar nan idan sunna raye a sanar masu tashin hankalin nan, hukuma dole zata shiga sannan dole Sarkin garina zai shiga, za'a je a tono kabarin koda an dora wani a kansa, za'a ciro layar nan cikin lokacin mafi sauki, domin ba zan yarda ba dukkan wani abin da ya dace sai an yi ANDIYA sannan a yiwa Amnah adalci, laifukan da kike tunanin nan mun tuba zamu ci gaba da neman tuba a wajen wanda muka yiwa su, kuma zamu jajirce da aikata wasu aiyukan ladan ama ba dai wannan da kike so ba!" Daga haka Bay ya saki hananyen Mah ya mike ya fice zuciyarsa na karra tukuki......, walahi ransa bai taba ɓaci da Ameerah ba irin na yau, kuma walahi sai ya yi mata matsanancin fushin da zai bata mamaki, sannan a dole zai dau mataki a kanta koda abin nan ya taba kwakwaluwarta zai fara nema mata magani, dan kuwa irin yadda ta daukaka lamarin rayuwarsu da zafi ya wuce misali! A lokacin da Bah ke cikin rikicin nan da Mah, YUSUF kuwa ya jima da karasawa falon gidansa baba ya ja ya tsaya ya kalli gabas, ya kalli arewa ya kalli kudu ya kalli yamma, gannin ya rasa alkiblar da ta fi masa sanyi sai kawai ya nufi dakinsa kansa na karra sarawa da matsanancin karfi ya dauro alwallah ya je saman salaya ya zauna hannunsa rike da carbi yana ja yana sauraron masalaci, domin yana ji yana ganni fita masallacin ya gagareshi saboda matsananciyar juwa da ciwon kai , gashi ko kari bai yi ba, sai abin ya yi yawa ya sa ya kasa zuwa masallacin sai a nan dakinsa ya ringa bin salolin nan har ya samu ta isha'i sannan ya lumshe idannuwansa daga kwoncen da yake yana jin wayoyinsa agaji suke nema, ama ya kasa tarda su , daga baya ma sai kukansu ya fara damunsa ya rasa yaya zai yi sai ya rintse ido kawai yana kama sunnan Allah a zuciyarsa *RAUDA* ta jima rike da wayarta a kunnenta da kuma plate din shayinsa a gefe, tana jin Muryar Mah dake cen kasa, wace ita take cikin wani halin tsaka mai wuya na tunani ta rasa yaya zata yi da tunani kuma rashin gannin ya dawo ya shiga damunta karshe dole ta dauki waya ta neme shi da kanta, ama ba'a dagawa, hakan ya daga mata hankali, ta sani duk rintsi in dai wayarsa na hannunsa yana daga kiranta, shi yasa ta yi kiran RAUDA tace ta je ta gano mata, shine ta dauki lipton dinsa gannin yana inda ta ajiye bai dauka ba, haka abincin rana da na daren sunna yada suke sai ta nufi dakin nasa da lipton din, ama kuma ta kasa shiga dan tsoron abinda zata tarar, ta yiwu ma tare yake da Matarsa A hankali Mah ta ce" baby, baya nan yayan baku ko?" Da sauri ta rintse ido ta kama ta bude ta shiga, sai kuma ta shiga kallon dakunnan da tunanin to ina zata duba? duba da daki biyu ne, a hankali kuwa sai ta ce" A'a Mah ban karasa ba, na bude nan din kuma kin ga ashe dakunnan biyu ne ina ne nasan?" Mah ta dan bude idannuwanta tana dan zarro ido ta ce" Baby dama baki san ina ne dakin mijinki ba? to ina kike ajiye masa girkin da kika ce ke dai kar a kawo maku abinci ke zaki yi?" RAUDA ta yi tsuru ta gaza amsawa Mah ta yi dan murmushi ta ce " ki duba wanda fitila ke kunne, idan kuwa duka a kashe ki murda kowane kawai ki shiga in sha Allah ba komai sai alkhairi a dakunnan" RAUDA ta dubi dakunnan, sai ta ga kwarai dayan da hasken fitila ta kasa, hakan ya sa ta sauke ajiyar zuciya ta nufe shi ta kama ta murda hadi da yin salama ta shiga baza idannuwanta a dakin tana sake yin salama har idannuwanta suka sauka kansa yana kwonce saman salayar nan wani iri kwonci a dukunkunne kamar dan karamin yaron dake jin yinwa A hankali ta ce" Mah, yana nan, ama anya ba barci yake yi ba kuwa?" Mah ta dafe goshinta , tunaninta na karra Tabatuwar y'arta kam babu abinda ta sani a maza, duba haka a tausashe ta ce" Duba mana mu gani?" RAUDA ta karasa ta ajiye lipton din dan nesa da shi kadan sannan ta zauna a hankali ta ce" Yayanmu, yayanmu, barci kake yi?" Mah ta saki murmushi tana sauraron ta , wai wani ƴaƴansu uhum A hankali ya bude idannuwansa yana kallonta, zaman da ta yi da yannayinta ya saka shi zubawa fuskarta ido yana kallonta "YAYANMU, ga wayar Mah ce" Ta fada tana cire dubanta a cikin nasa gabanta na faduwa a hankali ta ajiye masa wayar daf da hannunsa sannan ta sada kanta Sake Binta yake yi da kallo, da kyar ya budi bakinsa a hankali ya ce" Mah?" Mah ta sauke boyayiyar ajiyar zuciya tana waskewa ta ce " Dama ban ganka bane...., am dama ban ga wulgawarka bane tun dazun" A hankali ya ce" Eh, bani da lafiya ne" Da sauri RAUDA ta kalle shi tana jin kamar hankalinta zai tashi, Mah dinma muryarta da yannayin tashin hankalin ta ce" 😀😀😀 Ba eddtng fa😀😀😀😀😀😀😀 azl63 Muryar Mah da yannayin tashin hankali ta ce" Baka da lafiya? subahanallah, YUSUF na zo ne?" A hankali ya girgiza kai tamkar tana kallonsa ne ya ce" A'a, ciwon kai ne Mah, da sauki in sha Allah " Mah ta rasa me zata ce, murya a raunane ta ce" Allah ya baka lafiya, Please ba baby wayar" Kallon RAUDA ya yi, idannuwansu suka sake shiga cikin na junna, da ido ya mata alamun ta dauki wayar hakan ya sa ta saka hannunta ta dauka ta kara wayar a kunnanta a hankali ta ce" Mah" Mah ta sauke ajiyar zuciya itama a hankalin ta ce" Baby......, yaya jikin yayanku?" RAUDA ta sake kallonsa, a kwoncen da yake ba zata ce ga yannayin jikinsa ba, abinda ta sani shine bashi da lafiya, sai dai ba zata iya fadawa Mah haka ba, duba da ita dinma ba lafiyar ta isheta ba, duk irin tashin hankalin da take ciki ta gwamace ta hadiye a hankali ta furta" Da sauki Mah" Idannuwanta ba cika da wata irin kwallar da ta fito daga cikin kirjinta da tsananin tashin hankali ya danne "Please, ki kula da shi....., idan kin ga bashi da lafiya sosai ki sanar min komai dare, kin ji?" Mah ta fada a hankali tana ji a ranta ko menene yana tare da wace ke iya kulawar da shi da zuciya daya RAUDA ta gyada kanta ta yi saurin sada kan hawayenta suka zubo sharrrrrrrr har bata san Mah ta katse kiran ba Da sauri ta mike ta ajiye wayar ta nufi waje, hakan ya sa ya rakata da kallo kafin ya samu kansa da sakin lalausan murmushin da ya fito tun daga zuciyarsa, wanda irinsa ya nema ya rasa wunin yau kaf sai kunci da radadin zuciya Jim kadan ta dawo hannayenta dauke da kayan abinci ta karaso ta zauna daf da abin sallar A nutse ta zuba dan madaidaici sannan ta zuba ruwa mai dumi a cikin kofi tana kallon sa a hankali ta ce" Ka tashi ci, baka ci komai ba fa yau" Shima kallon nata yake yi, a hankali ya ce" Azumi nake yi ai" Ta turo baki tana kallonsa ta ce" An yi isha fa, Please ka tashi" Idannuwansa ya lumshe ya ki tashin, hakan ya sa ta rasa yaya zata yi da shi, tana so ta taimaka ta kama hannayensa ta tashe shi ama ta rasa ta ina zata fara, wani irin nauyi take ji a ranta da kunya, tana ji a jikinta ba zata iya cicibar hannayensa ba ta taɓa da nata hannayen kai tsaye ba, sai kunyar hakan ya sakata sada kai kawai tana jiran gannin ikon Allah "Ama, ai ba haka Mah tace ki min ba ko?" Ya fada a hankali yana kallonta Da sauri ta sake kallonsa, sai kuma ta sake sada dubanta a hankali ta ce" Ban san yaya zan yi maka ba" Yana kallonta ya ce" Kamani zaki yi ki dagani sai ki bani abinda kike so in ci a bakina , haka ake yiwa marar lafiya" RAUDA sai ta ji tamkar zata nutse a zaunen da take, ta dube shi ya fi a irga, karshe ya tafka tagumi da kyar ta ce" Ban san yaya zan yi ba, ba zan iya ba, dan Allah ka tashi" "Bani da nauyi fa" "Ni kunya nake ji" Ta fada cikin subucewar harshe, a dole ya sa ta ji kunya har ya fada cewar kunyar take ji, shi yasa ta rufe fuskarta da sauri bayan ta ga ya tsura mata ido yana yi mata kallon da bata so Kansa ne ya karra daurewa, dan ya tabatar da abinda take nufi sai ya tashi ya zauna din, ya miko mata hannunsa dan ta bashi ruwan mai dumin dauko ruwan ta yi ta miko masa, a nutse ya kama ruwan hade da hannunta ya rike Da sauri ta kalle shi, ta ja hannunta ama ya ki saki, ta sake ja ya ko saki, nan da nan sai hankalinta ya nemi tashi, karrara tsoronta ya bayyana hadi da tashin hankalinta, har hakan ya hadasa mata da dan barin hannu kadan, wannan karron shine na biyu da hannunta ya hade da na wani hadewa ta kirki din nan ba ta a yi fada ba, hakan ya sa tsoronta kasa buya har sai da ya dubeta da mamaki ya ce" Bari mana, me yasa kike haka sai kace ba ke kila haifi Abdul ba!" Da wani mamakin da kuma sauri ta dube shi, kai, Abdul kuma? ita RAUDA ce ta haifi Abdul?, sai dai ta kasa magana saboda kin sakin hannunta da ya yi, shi da yace ba zai iya tashi ba harda janyota daga zaunen da take ya shiga shan ruwan zafin dake hannunsu a hankali yana sake yi mata kallon nan da bata so Ajiyar zuciya kawai ta saki ya sada kanta tana kallon abincin har ya ga dama dan kansa ya saki hannun nata ya ajiye kofin ya lumshe idannuwansa gumi na tsatsafo masa kadan Shayin ya fara sha, shima sai da ya jima a cikinsa sannan ya dan taba salak kadan ya mike a hankali ya nufi hanyar kofar yana zuwa ya datse kofar ya juyo a nutse ya karasa wajen sif dinsa ya dora ky din cen sama sannan ya juyo yana cire jalabiyarsa RAUDA dake tsaye rike da kayan abincin ta yi gaggawar juyawa muryarta na dan rawa ta ce" Am, ban fita ba fa, ka rufe kofar da Ni fa" Dama ita yake kallo , wato diyar Mah ta gama raina masa hankali, ko kicin zata shiga fa ba hijab take shiga, ama zuwa wajensa ta dankara hijab, shin ko ba'a bata sadakinta a hannun dake iya tabatar mata shin waye a wajenta bane? Bai amsata ba ya dauki tawul dinsa ya wuce bayi , dan wankan nan da ya saba idan har bai yi shi ba ba zai iya jin dadin jikinsa ba, duda irin yadda yake jin jikinsa da abin zazabi sai ya yi Yana shiga ta ajiye kayan da gudu ta zo ta shiga dagen dauko ky din, ama cikin ikon Allah ta gaza kaiwa wajen da yake da sauri ta sauka tana dube duben abin hawa, dan hankalinta ya kasa daukan tana ji tana gani ya shiga bayi daga shi sai zani ya fito ya sameta a dakin nan, to ta kalle shi ta yaya? kai mutumen nan walahi bata san me yasa baya jin nauyin mutane ba sam kujerar dake ajiye wajen gadon ta dauko da kyar dan nauyi ne da ita ta kawo ta ajiye sannan ta cire hijabinta gudun kar ya kayar da ita ko kar taje ta fado ya shaketa Hayewa ta kuma yi ta ringa dage ko zata cafki ky din, a haka ya fito daga bayin ya yi turus yana kallon ikon Allah da sauri ta diro daga saman kujerar ta yi tsuru tsuru tana kallonsa hadi da dan nuna wajen tana sosa goshinta ta ce" Dama, ky din ne zan dauka wai kar na baka aiki na bude kofar na........." Da wani saurin tana katse maganarta ta matsa sosai dan gannin kamar wajenta ya nufo ai Bata idasa tunanin nan ba ya janye tawul din dake jikinsa A haukace ta juya kirjinta na wani irin dokawa tamkar zai fito ta bakinta ya fadi, gaba daya jikinta ya dauki rawa ta rintse idannuwanta, ba wai haka yake karbar ungozoma ba fa, ama kuma kasantuwarsa da gajeran wandon a matsayinsa na katon mutun din da ta hadu da shi rana tsaka dole ya gigita tunaninta Rigar barcinsa ya dauko da dogon wando a nutse ya saka a jikinsa sannan ya bude wajen turarukansa ya dauki mai sanyin kanshi ya shiga fesawa jikinsa a nutse har ya gama sannan ya ajiye ya juyo ya harde hannayensa yana kallonta a hankali ya ce" kika ce me?" Da sauri RAUDA ta juyo tana kallon kasa kasa wajen kaffafuwansa, gannin abin tufafi a jikinsa ya saka ta dago tana kallonsa a raunane ta ce" Cewa na yi ka bude min in tafi in kai kwanukan kicin in wanke su in share kicin din kuma in yi aiki mai yawa a cen din" Baki ya tabe ya bi abincin da kallo a rufe ruf, sannan ya dawo da dubansa, harda hade hannaye ta yi kamar wace ke tsoron wani abin A nutse ya shiga takawa inda take tsaye, ita kuwa da yannayin tsorata da shi take yin baya baya har suka dangane da jikin abin gadonsa Rigar dake jikinta ya bi da kallo, mai siririn hannu ya kai idannuwansa har wajen wuyanta sannan ya sauke a fuskarta yana kallonta a hankali ya ce" Me kike tunani wai?" RAUDA ta yi tsuru tsuru , sai ta bude baki sai ta rufe ta fitar da wani dan sauti sauti a cen cikin makogwaronta wani "UM" ido kuwa sai mucik mucik take masu tana gannin gaba daya ya kare bata gaba "Tell me, kina tunanin zan yi hvng sx da ke ne yanzu?" ya fada a nutse yana kallonta a rikice ta furta " Astagfrullah, astagfrullah kai, innalilahi wayo Ni walahi ko a kwakwaluwar Makiyina ban kawo tunanin nan a raina ba, haba dai yayanmu ne kai fa, me hadina da wannan abinma ni? kawai dai tafiya nake son yi daga nan din gaba daya Ni " Sosai yar kwalar da take sharewa na ta shiga ukun nan ta sake saka shi zuba mata ido, kafin ya sauke wata irin ajiyar zuciya hadi da wani huci mai sanyi , a hankali ya ce" To amanar da Mamanki ta baki fa ?" RAUDA ya karra share hawaye dan abin nan ya yi mata zafi a zuciya, tsakani da Allah ita ai ba haka take ba, bata san wannan abin ba kuma bata sakawa ranta shi ba, ita ba ruwantama da wannan maganar, ita mai yin maganar nanma a wani dan is haka dai take kallonsa, shine zai wani ce tace? Murya a raunane tace" To ai ka warke" Kai ya girgiza yana murmushi yana sake kallonta da mamaki ya ce" A'a, ban warke ba, kuma ina ji a jikina sosai banda lafiya, zo ki ga yadda zuciyata ta kumbura " A tsorace ta kalle shi, zuciya? kumbura?, yanzun kam da kanta ta iya binsa bisa hudubar Tata zuciyar hankalinta na neman gushewa daga gangar jikinta saman gadon ya zauna a hankali ya bale boturan rigarsa na sama yana kallonta ya ce" Kawo hannunki ki gani?" Sai da ta jimke hannun nata, sai kuma ta dauko yana rawa rawa ta dan miko daga nesa tana kallonsa tana jin hankalinta na tashi, kennan shi yasa yake kwonce bawan Allah zuciyar ce ko? ita dai ta shiga uku, sai Abdallah ya fado mata a rai, hakan ya sa da kanta ta saka hannunta cikin nasa hawaye na bale mata tana jira ya kai hannun nata dan ta gani? bata san abinda zata iya yi masa dan ta taimaka masa ba, sai dai ta san ba zata iya tafiya ta barshi ba A hankali ya janyota gaba daya ya cirata daga kasa ya ajiyeta saman ƙafarsa sannan ya sakata jikinsa ya rungumeta sosai a jikin nasa Da farko zabure zabure ta fara, daga baya ta ringa kiciniyar kwacewa, a karshe ta yi sororo ta gaza kwace kan nata sai ta ringa sauke ajiyar zuciya tana jin bugawar zuciyarsa jikinta na karra yin laushi dan ta gama yarda cewar zuciyarsa ciwo take yi "Me yasa kike kuka da zarar na maki magana, bayan ke din ba mai saurin kuka bace a wani wajen?" Ya fada cen kasa kasa cikin kunnayenta, hakan ya sa ta lumshe idannuwanta hadi da yin lamo ta kasa kwacewa, ta kuma kasa wani yunkurin A hankali ya ce" Ke ce maman Abdul?" Kirjinta ne ya karra dan dokawa, a hankali ta yi yunkurin tashi, yanzunma ya hannata yana rike da ita din nan kasa kasa ya ce" Just answer me *Yes or no* ?" RAUDA ta dora hannunta ta dago da kanta da dan karfin da ya rage mata, har yanzu jikinta na rawa tana kallonsa ta ce " Dakina nake son tafiya Please" Idannuwansa ya lumshe, a hankali ya kama abin gadon nan ya kashe fitilar dakin sannan ya mike da ita ya kwonta sosai da ita a jikinsa ya zamo bayanta ke jikinsa fuskarta a saman hannayensa A hankali yake kara shaƙar man gashinta, muryarsa cen ciki ya ce" Ki daina kokowa, kar ki sa na kai inda bani da niya a yau, Please ki bar mu mu yi barci *BABY* " 😍😍😍😍😍😍😁😁😁 *MAGANIN KARA KIBA 3IN1* *Ina meneman kiba ido rufe Kuma tanason maganine ingantacce Wanda baida illah kokadan to tazo gadama tasamu yar uwa indai kibace da gyaran nono dakara hips toga Mganinmu nan 3in1 cikin kwana 7 kacal👌🏻 zakiga yadda Zaki fara murmurewa insha Allah mungwada mungani munbayar angwada munsayar angode insha Allah kawata Zaki godemin da 3500 dinki kinhuta da gorin rashin kiba munan cikin Gombe Kuma munatura kaya ko ina kedai tuntumebi ta Whatsapp ko kikirani Kai tsaye ta 08030861857 sai kunzo🥰* *MAGANIN HIPS* *Wannan Maganin anyisane tamasu neman hips sunsha wannan sunsha wannan to gatamunan insha Allah guarantee nakebaki hajiya inada yakini akanta matsala indai tarashin hips ne to anwuce gun 3500 kacal kinhuta kijuya kiwarwasa kisaka kayan gayu kijuyawa Oga yayikallo kawata har yanga saikinmasa ninafadamiki wannan nemeni kisamu naki 08030861857* *MAGANIN NONO* *Itama akwaita me inganci kamarta 3in1 data hips wasu suna korafi nifa nono kawai nakeso yaciko yayi bulbul gwanin sha'awa yadda Oga zaiyaba nasa breast cup suzauna das Amman abun yacitura Nasha Nasha magungunan Amman haryau ba chanji to ganamu Nan yakine ne Dani akansa ba Dan kadanba alhamdullahi duk Wanda yasaya saidai godiyace tsakaninmu kema zokigwada Kuma kigodemin location Gombe 08030861857* azl 64 *MAGANIN KARA KIBA 3IN1* *Ina meneman kiba ido rufe Kuma tanason maganine ingantacce Wanda baida illah kokadan to tazo gadama tasamu yar uwa indai kibace da gyaran nono dakara hips toga Mganinmu nan 3in1 cikin kwana 7 kacal👌🏻 zakiga yadda Zaki fara murmurewa insha Allah mungwada mungani munbayar angwada munsayar angode insha Allah kawata Zaki godemin da 3500 dinki kinhuta da gorin rashin kiba munan cikin Gombe Kuma munatura kaya ko ina kedai tuntumebi ta Whatsapp ko kikirani Kai tsaye ta 08030861857 sai kunzo🥰* *MAGANIN HIPS* *Wannan Maganin anyisane tamasu neman hips sunsha wannan sunsha wannan to gatamunan insha Allah guarantee nakebaki hajiya inada yakini akanta matsala indai tarashin hips ne to anwuce gun 3500 kacal kinhuta kijuya kiwarwasa kisaka kayan gayu kijuyawa Oga yayikallo kawata har yanga saikinmasa ninafadamiki wannan nemeni kisamu naki 08030861857* *MAGANIN NONO* *Itama akwaita me inganci kamarta 3in1 data hips wasu suna korafi nifa nono kawai nakeso yaciko yayi bulbul gwanin sha'awa yadda Oga zaiyaba nasa breast cup suzauna das Amman abun yacitura Nasha Nasha magungunan Amman haryau ba chanji to ganamu Nan yakine ne Dani akansa ba Dan kadanba alhamdullahi duk Wanda yasaya saidai godiyace tsakaninmu kema zokigwada Kuma kigodemin location Gombe 08030861857* Magana ne yake yi cen cikin kirjinsa, kuma idan ya fada din sai nata kirjin ya amsa, a dole ta yi lamo tamkar wace ke barcin har sai da barcin ya dauketa, wani irin barci da farkonsa ya yi mata nauyi ainun, karshensa ne ya zame mata marar nauyi da dadi A hankali hannunsa da take karewa da karfi ya saka ta bar hannun nasa a jikinta A hankali ya dan dago ya tokare hannunsa daga baya ya zubawa fuskarta ido Kirjinsa ke bugawa har ya wuce misalin ka'idar abinda zai iya tankwasawa ko ya tsawatarma.....shi kam ya yi rayuwa cikin zagaye zagayen wannan abu da ya lakabawa Azal ashe mai tunkudashi cikin ce bata karaso ba, gashi yanzu da girmanshi da komai ya san cewar nutsuwarshi itace kuma idan ya yi wasa tsaf zai rasa ta? ya salam gatanan fuskarta tamkar ta jaririn da cikinsa ke cike lafiyarsa kalau barci ya dauke shi, shar da ita barcinta take yi hankali kwonce, babu abinda ya damu RAUDA a rayuwa, sai ya ji inama ace shima irinta ne! ba nauyin kowa ba damuwar kowa a duniyarta sai ta abinda ba za'a rasa ta daidaikun mutanen da basu gaza irgen yan yatsu ba? Ajiyar zuciya ya sauke ya sauka ya koma bayi ya dauro alwallah sannan ya sake hawa saman salaya ya shiga gabatar da nafilarsa Bayan ya gama ya zauna yana ta adu'a da karatun Alqur'ani ya gama ya shafa ya mike ya dauki karamar wayarsa ya koma saman kujerar dakin ya dannawa Shaheed kira ya masa kira na uku sannan ya daga murya shake yana fadin" Kai Ni fa yanzun kuma lokacin ido ne, kai baka barcin dare ne?" Murmushi ya yi shima kasa kasa ya ce"Magana nake so mu yi" ido Shaheed ya sake budewa da kyau yana mikewa daga kwoncen a nutse ya zauna ya dan jima jim sannan ya sake bude muryarsa ya mike ya sauna a gadon yana fadin" Lafiya kake magana murya a shake?" Lumsasun idannuwansa ya kai wajen da take kwonce lamo, duda duhun da ya sakawa wajen bed din ama abin hasken bayi kadan na dan haska yannayin kwonciyarta, kasa kasan ya ce" Baby ke barci" Dan turus Shaheed ya yi bayan ya kuskure bakinsa ya zubar da ruwan ya dawo ya zauna ya ce" Amnah?" YUSUF ya dan cije lebensa ya ki bashi amsar nan dan ya sani sarai so yake yi ya kaishi makura, a hankali ya ce" Man, ya tabata fa, abin nan" Shaheed ya yi wani irin shiru yana dafe gaban goshinsa zuciyarsa na kiyawa, a hankali ya furta" Ya rab" YUSUF ya sauke ajiyar zuciya yana sake lumshe idannuwansa Shaheed ya ce" Ina fatan, ka dauki hakan matsayin kadarar rayuwarka baka ɗorawa kanka wata damuwar ba?" Wani murmushin YUSUF ya yi yana sake dan shafa gashin kansa, hakan ya tabatarwa Shaheed tabas Yusuf ya dauki wannan abin matsayin dole ne ya ga haka tunda har bai zauna waje daya ba a da A tausashe ya ce" Idan ka yi haka, kamar ka nuna ilimin ka sanin ne kawai, ba zaka yi aiki da shi ba....., ka ga rayuwa babu abinda bata zuwarwa bawa da shi, Ni in ce mi a kan tawa rayuwar? Ni na gina rayuwa da ita har mun haihu ama a kan shirme ta lalata komai, in ba dan mahaifinta ya yi tsaye ba da harta sunnan gidansa ta lalata, ka ga dan Adam ne keda haka, dan adam a kan kadan sai ya bata da yawa, inaga a yi hakuri da kadarar nan shine ya fi zama alkhairi " "Na sani, kuma na yarda da haka, but Mah tace za'a zauna da ita a yadda take Man" ya fada kasa kasan yana lumshe idannuwansa shima ido ya bude sosai ya ce" Ban fahimta ba, tana nufin zama na aure?" YUSUF ya dan gyada kansa tamkar yana gabansa, kasa kasa ya ce" Na Bara maka sako a amail dinka, dangane da iyayen nata " Mikewa ya yi da sauri ya karasa wajen da computarsa ke ajiye ya danna ya shiga dadanawa yana zuwa har ya kai wajen da yake son zuwan, YUSUF na jinsa kuma ya gane sakon ne yake son karantawa shi yasa ya yi lamo a saman kujerar yana sauraronsa har ya gama karantawa ya ringa jin salatinsa a nutse sannan ya ji ya shiga magana a tausashe kamar haka" Dole hukunci zai hau kansu, daga ita har shi la'ananen!, dole za'a sanar da hukuncinsu, sannan dole za'a sau yarinyar nan, ba matar SARKI bace!" Shirun da Yusuf ya yi ya saka Shaheed fadin" Ba wasa nake yi ba, ba zan kyale ba fa, ba zan iya kyalewa ba, ba matar aurenka bace, rashin jin magana na rigima daban wanda Allah ke jarabtarmu da mata masu halin nan, wannan lamarin daban, da ace wasu yan tsirakun ne sai a daidaita zaman, ama abin da yawa , abin da yawan gaske da kuma girma, ita da kanta rayuwar garinka sai ya gagareta idan abin nan ya fita , bale ita din mutun ce mai janyowa kanta makiya da kanta, inaga abinda ya dace a yi shine a maida hankali a zartar da komai kafin ta sakankance!" "Maganar Mah ake yi Shaheed, maganar Mah ake yi, ka san Wacece Mah a rayuwata, a duniyata, zan iya rantse maka ni dai ba zan taba tsallake maganarta ba tunda ba sabawa Allah ta yi ba,kuma na san kaima ba zaka sa a tsallake din ba......, ka san me yake damuna? Shaheed ka san menene ya fi damuna?" Shaheed da jikinsa ya karra yin sanyi a hankali ya amsa shi da a'a YUSUF ya ce" Abinda yake damuna Amnah sunnanta uwar gidana a cikin Matana, idan tana matsayin matata dole zamu samu iyali da ita in dai tana haihuwa kuma in nima ina haihuwa....., yaya zata tarbiyantar da yayana bayan ita dinma bata da tarbiyyar.....?, har yanzu bata yarda tana cikin aikata laifin da bai dace ba bale ta fara tuba, gidana ta sanyo min dan daudu har dakinta na barci, tana iya tubewa a gabansa bilahilazi!" Shaheed ya dafe kirji dan irin yadda wani abu ke masa zuga a ciki, shi fa da ace maganar nan ba Mah ciki, walahi walahi a gobe sai ya san abinda ya aikata aka fito da kowa aka yi masa dukan tsiya kafin a bashi hukuncin da ya dace, dan a yanzu shi bai cika bada hukunci ba duka ba, zane mutun ake yi da dukan da zai gigitashi sai a hauda da hukunci, shi yasa iya shege ya ragu sosai a Damagaran, "Nd......nd....... Shaheed bana tunanin zan iya auren wata na hada da wancen dake barci na iya yin adalci......, ka ga an jima da kawar da maganar wai dole sai an yiwa sarki mace biyu, ko hudu, an dawo duniyar idan zai iya, Shaheed na riga na san in na yarda na karra mata wata rigima zata yi ta yi, kuma Ni rigimar ce bana so walahi du daga min hankali take yi" ya karashe a sanyaye Shaheed ya yi shiru na yan sekwani, a hankali ya ce " wai wace ne haka?" YUSUF ya ce " Baby mana wace zan ce in ba ita ba" Shaheed ya sauke numfashi a dole yana dane dariyarsa, sai dai kiri da muzu dariyar nan ta ki dannuwa sai da ya yita kasa kasa yana fadin " Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, kai bawa, bawa? in ba dan gagawa ta bawa ba da ya cinma abu da yawa, ka duba ka ga irin dauki ba dadin da muke yi da kai, idan na ambata maka soyayama sai ka nunan yatsa, ashe Azal din ta idasa cin maka har kana fada baki sake? cewa fa ka yi ba zaka taba yafe mata ba? a kan me zaka yafe mata? kar ka yarda fa man" YUSUF ya yi tsittttttttt yana sauraronsa, a hankali ya yi murmushi ya ce" Ai Allah yana son mai yafiya, ka ji tsoron Allah hadani zaka yi da iyalina? ka ga sai an jima dilla" Gannin da gaske kashewa zai yi ya ce" zan ajiye maka sako a amail ka duba Please, kuma ka ga NAJEEBA tace zata zo ta yi Barka da tarewa, ama anya zaka bari a ga wama kace?" Yusuf hankali kwonce ya ce" Baby, baby ne sunnan" Shaheed ya sake saka dariya a dole, dan walahi bai tana gannin marar kunya irin YUSUF ba, uhum lalle, dama ya kyale shi wani cika da batsewa wani alwashin ba zai yafe masa ba ya bashi lokaci ne , gashinan abin ya zo ya koma wata y'ar murya kamar ba shi ba, a haka suka yi salama Shaheed ya shiga loda masa sakon da zai Bara masa din dan idan safiya ta yi ba lalle ya iya samun lokacin aika sakon ba, abu daya ya sani YUSUF sarki ne, ya kuma yarda da sarautarsa dan a hawansa zuwa yanzu ya jinjina masa fiye da kima, Yusuf ya yi rawar gani a garinsa yana cikin yi, Yusuf bai dogara da albashi gwamnati ba irin na wasu sarakan, a yanzu haka tun hawansa har zuwa yau bai san me gwamnati ke zuba masa ba matsayin albashi, shi yasa a lokacin da ake rigimar sarauta wa za'a Hauda yace sunna da sarki sama da wanda zai iya rike su ne? ai nasu da sarki sai wanda zai iya rike su, idan har rayuwar suke son gannin cenzawarta, kwarai Hajia baba ta yi gaskiya da tace da su me suke jira? duk wanda yake da ja ya kwatanta ya kawo wanda ya fi shi, YUSUF tun bai zama sarki ba yana taimakawa talakawan garinsa a boye bale da ya zama sarki, karami ne a cikin manya mai manyan kudade a dole rana tsaka manyan suka ce da MALEEK *BABA* YUSUF kuwa murmushi ya yi yana karra jin sanyi a zuciyarsa A rayuwa ko waye kai, ya zamo kana da abokin sirri, wanda idan dadi ya samu zaka tunkare shi da shi kai tsaye haka kuma wahala, tsakaninsa da shaheed sukan yi kiran tsakiyar dare dan kawai su yi jayayya a kan ball, haka kuma sukan yi dan su yi maganar sirrin su a tsakaninsu, gaskiya daya ce, amana daya ce, sunna shawartar junna da shawarwari masu kyau sunna kuma amintar junna da zuciya daya A nutse ya koma saman gadon nan, cikin dabara ya dorata saman kirjinsa a hankali yana shafa kanta har barci ya fara fizgarsa , a kasan zuciyarsa yana yarda da akace abin nan fa na dadi ne, bai taba tunanin shi YUSUF zai iya wayar gari, gashi ga RAUDA a daki daya wani abu ya hanna shi far mata ba, sai gashi yannayin da zuciyarsa ke ciki a yau ya ki wani yunkurin dan ba zai so ya sauke mata wani fushi ko tashin hankalin a kanta ba, zai fi so ko menene ya zo masu a nutse yadda abin zai zama baban tarihi a rayuwarsu....da wannan barcin ya dauke shi shima mai sanyi da nutsuwar dake jikinsa har kiran sallah ya tashe shi, ko nace ya tashe su gaba daya Irin yadda yanzunma take boye fuska ya saka shi nishadi , irin yadda take hade jikinta tana murzar yan yatsu ya saka shi yi mata kallon y'ar shilar amarya har a cikin ransa, sai kuma ya ringa jin tamkar zai yi bincike a duniyarta, domin tunda yake bai taba motsi da nufin bincikar Wacece RAUDA ba, sai iya abinda ta fada da bakinta a ranar da suka je gidan su shi da Bah da Mah, da wanda ta fada bayan ta gama koke koken uncle din ta, wato dai sama sama gefe gefe ya san RAUDA, ya hanna kansa bincikar Wacece ita dan baban tsoronsa kar garin bincike binciken ya bincikawa kansa ciwon da zai zame masa ila a rayuwa Da wannan ya fice a dakin ya nufi masalaci, itama ta dauki hijabinta dake kasa da kwanukan nan da gudu gudu ta gudu nata bangaren ko wayarta bata iya tsayawa dauka ba, tsoronta daya kar ya kuma samun ta a dakin ya hannata zuwa nata dakin, wannan abu da ya aikata mata jiya zuwa yau kuwa ya gama like mata a zuciya, zuciyarta banda kiran d'an Mah ba abinda take yi a boye Kamar yadda suka saba daga masalaci shi da Bah suke nufowa bangaren Hajia baba hakan ce ta faru yauma Sai dai a hanya Bah din ya sanar masa abinda ya faru a jiya shi da Mah da kuma abinda suke da niyar yankewa shi da Hajia Ya ji komai, ya kuma fahimci komai, ama ya kasa cewa komai har suka karasa bangaren Hajia suka tarar da Mah a nan din a bangaren na Hajia, da duku dukun nan, hakan ya basu mamaki su duka, har ya sa ya karasa da sauri gabanta yana dukawa da kokarin duba jikinta yana gaisheta da tambayar menene ko lafiya? shi kuwa BAH ya dauke kansa ɗan ya san sarai abinda ya hannata barci har ta yi samakon nan ya kuma karra daurar niyar matse mata lamba har sai ta saduda da kanta ta nemi sulhu, ya gaji, ya gaji ainun da ganninta tana wahalar da kanta bayan Addinin Musulunci ba haka yake ba, addinin musulunci sauki ne da shi sosai, kuma Allahn da ya halicemu gafurun rahim ne Hajia ta saka sandarta ta zunguri kansa tana fadin" Kai dilla in ka ganta a nan ai da kaffafuwanta ta zo , sai ka tambayi mai dakin ko nice na summa ta zo ko? kai dai akoy sarkafar uwa!" YUSUF ya juyo yana kallonta ya tabe baki kasa kasa ya ce" Wai wani ko kece kika summa, kina nan zaune sai kashe min iyaye kike , an ki a duba kin da wani hijab dinta haba a karkace" Mah ta saka carbi zata kwada masa da sauri ya karasa kusan Bah ya zauna yana harde hannayensa ya sakarwa Hajia harara wace ke dariya tana fadin" Ja'iri da ka tsaya mana ka ga yadda y'ata zata zane min kai" Da raha sosai wajen ya fara, sannan suka koma jimamin lamarin nan, inda Hajia ta tabatar da abinda suka yanke ita da Bah, kuma Mah ta tabatar da ta yarda sannan shima ya tabatar da yana tare da abinda aka yanke din kafin ya mike ya nufi bangarensa, hakama Bah ya yi ficewarsa aka bar Mah da Hajia, Mah ta mike ta nufi kicin din Hajia dan ba zata koma bangarenta ba sai komai ya daidaita kuma Yana komawa ya nufi dakin RAUDA kai tsaye, dan ya tabata bata dakinsa A lokacin Rauda ta yi wanka tuni ta yi sallah ta shiga saka turare a dakin nata da nufin gamawa ta shige kicin dan ta sama masu abincin kari ta ji ana buga mata kofa ta dan yi jim dan tunanin ko waye, hakan ya sa ta nufi kofar ta kama ta bude tana buɗe baki ta ce" Wa.............." Sai kuma ta yi dif a hankali ta yi shiru tana kallonsa Shigar jikinta ya fara bi da kallo, da kwalin idannuwanta da jan bakin da ta dan shafa madaidaici ya sauke dubansa a kan hannayenta da ta rungume a kirjinta tana kallonsa a hankali ya ce" Morning aunty" Ido ta kwalalo tana sauke hannayenta da wata irin kunya ta sada kanta ta ce" Lah yayanmu, ban kai da gaisheka ba fa ina mamakin ganninka a nan ne ban san me ka zo yi ba yi hakuri yayanmu, ina kwana an tashi lafiya?" Shigowa ya yi da kyau ya ce" An tashin dai, lafiya kuma ai sai na zama ango, abinda ya kawo Ni kuwa zance na zo " "ikon Allah, innalilahi " Ta fada a hankali tana zagaye shi ta karasa ta dauko hijabinta ta karaso zata wuce hannunta daya ya kama ya janyota a slow ta zo gabansa da dayan hannunsa ya saka ya tareta yana dage gira ya ce" Kar ki gogeni mana kato da Ni, ke wai daga bugawa sai ki wani bude ba hijab dan kin ganni ki saka hijab, to mamanki bata ce maki ba hijabi tsakanina da ke bane ko kallon katon kwarata kike min" "Na shiga uku" Ta fada tana rintse ido Ya sake tare fuskarta ya ce" Mun shi shiga uku dai, ina zaki je dan na zo sai kace kin ga mai kwasar zancenki?" " kicin fa zan je yayanmu" Ta fada tana raraba kalmar, dan ya fara fin karfin ta walahi "Mu je, ama ki ji tsoron Allah ki daina min halayar nan, sai in mance kece fa, ji wani yayanmu, wata magana a sanyaye bayan na san ba tsorona kike ji ba!" Ya fada yana juyar da ita ya nuna mata hanyar kicin din, a dole ta ja ta tsaya tana kallonsa yannayinta na nuni da rauninta a kansa, jiki ba karfi ta ce" Kicin fa na ce zan je?" Da girarsa ya mata alamun eh sai me?, hakan ya sa a sanyaye ta ce" Kai Sarki ne YUSUF, me ya haɗaka da kicin? dan Allah ka yi hakuri idan yinwa kake ji yanzu yanzu zan kawo maka ko menene in sha Allah" Fuskarta ya fara tsarewa da ido, sannan ya sauke duban a kan lebenta.............. Shi yasa ya guji sarauta............ Domin shi mutun ne da ya damu da ahali......., a lokacin da Bah ke nuna masa ya dace ya daina zuwa wajen Hajia da wajensa da Mah koda yaushe ya nuna masa shi yasa ya sa aka yi masa hanyoyin nan na baya.....domin ya rayu ne a haka, baya tunanin sarauta zata masa iyaka da iyayensa....uwa uba da RAUDA. Bai san wani yare zai yiwa RAUDA a yanzu ba, abu daya tak ya sani shine idan kicin take zai iya zuwa ya bare mata tafarnuwa, idan mak'up zata yi yana iya rike mata jaka har a gama, yana iya tayata zabar sutura a shago idan hakan ta kama, yana iya tayata kada miya.........'.. Murmushi ya yi yana kallonta a hankali ya ce" Yinwa nake ji" RAUDA ta sada dubanta daga nasa kasa kasa ta ce" Ohk, me zaka ci,me zan dafo?" "You.................." Ya fada daga cen cikin makogwaronsa A zabure ta kalle shi, tana ruko ido, hakan ya sa ya dan shafa kansa yana murmushi a hankali zai yi magana AMNAH dake nemansa a fujajan , har hanyar fita ta je dan ta je nemansa bangaren Mah Taj ya hannata fitar, shine ta nufo bangaren RAUDA duda zuciyarta na tabatar mata me zai yi a cen? Sai dai kiran da mahaifiyarta ta yi mata ya sa take neman nasa a fujajan dan so take ta je ta ji, wai an kawo samaci daga office din shugaban yan sanda ana neman iyayenta? ko lokacin hawa aikin bai gama cika ba ai, waye zai kai karar iyayenta ita a garin Tsatsunburum? ko waye bako ne, kuma shi shugaban yan sandan yau sai ta nuna masa sunne manyan garin, ta tabata dan bai san ita ke auren MALEEK bane ya kawo wannan gangancin, sai dai tana zuwa ta gansu a irin tsayuwar nan, da kuma irin yadda murmushi ke fita a fuskarsa Maganarta ke neman bacewa a bakinta, ta kai ruwa ta kai mari ya fi a irga bale da ta ga ya zuba mata ido yana jiran ji daga bakinta hakama Rauda da ta juyo har sai da bayanta ya hadu da kirjinsa ta dan matso gana kadan ita dinma tana kallon Amnah din da jiran jin abinda ya kawo ta har nan wajen AMNAH ta rintse idannuwanta saboda kanta da ya sarra, ta dantse lebenta ta sake saka idonta a cikin nasa da kyar ta iya kankaro magana a bakinta harufan ba kaifi ta ce" Duk yadda ta so yin tamkar bata ga RAUDA ba abin gagarar idannuwanta ya yi da bakinta, duk yadda ta so sharewa ta nuna wajen mijinta ta zo ta gaza hakan, har ta kasa tankwasa harshenta tana duban RAUDA da manta abinda ya shiga tsakaninsu saboda kishin dake ranta nata ta ce" Me kike yi a nan da mijina?" RAUDA ta sake zuba mata tana kallonta, a zuciyarta kuwa tana ta maimaita adu'ar da ta koyawa kanta a kan lamarin Amnah, domin ta zauna ta yi wani dogon tunani dan ta gano menene wutar tsanar dake ruruwa a zuciyarta a kan Amnah, me ta yi mata da zafi bayan zagin rashin kunyar da rashin tarbiyyar da ta nuna mata bata samu ba a gidansu? ta gane daga su din dai sai auren wannan bawa ta ga gama yarda cewar shi din gagarumar rikicin rayuwarta ne, shi yasa ta zauna ta yiwa kanta shawarar in sha Allah zata koyi dauke kanta a kan wannan matar domin bata tunanin in har tace zata ci gaba da biye mata zasu haifi d'a mai ido, irin yadda idan ta riki wuyanta take ji a ranta bata so ta saki kar wata rana aikin gangan ya kaita aikata dana sani a kan abinda yake nata itama kuma halalinta tinowa da ta yi natan ne halalinta ya sa ta ji zuciyarta na son daukan zafi da shi bayan yanzu yanzu tamkar ta fito masa a mutun ta sanar masa labarin zuciyarta, a kallon nan da suka yiwa junna a ranta babu abinda bata ayana na tarin kaunarsa da muradin sanar masa ba Cire kanta ta yi a kansu baki daya bayan ta yi masu kallon tare sannan ta juya da nufin tafiyarta Ya jima da gane karatun yarinyar nan koda da harara ta yi shi, hakan ya sa ya kasa kyaleta ta tafin ya riko hannunta ya dawo da ita yana kallon Amnah a tausashe ya ce" Amnah, yaya zaki fadi magana irin wannan?, Rauda fa matata ce, ko a dakina kika ganta ta zo dakin mijinta ne bale nan din dakinta ne fa" A tausashe ya yi maganar, ama sai da ya sa hawaye suka taru a cikin idannuwanta, hannayensu ta bi da kallo ta sake dora dubanta a kansa, matarsa? har fadi yake yi wai wannan yarinyar mai fada kamar mahaukaciya ce matarsa? ai walahi ko zata tafi tsirara sai ta raba auren nan nasu, ai wannan ba sa'ar su jera bace Bama bale ace su yi kishi, banza da ita! Itama a tausashen sai dai tana wani daga ido ta ce" Magana nake so mu yi" YUSUF ya sake riƙe hannun RAUDA dake son janyewa ta tafi, dan bata son abinda zai kuma hadata da wannan mai uwa da uban, salon a tabata kadan ta tarawa mutane iyayenta , ita kuwa da nata basa duniya sai dai ta kalle su ko? Allah ya sa Allah ke bada uwa da uba, ita marainiyar itama ya bata masu hankali da tunani ma kuwa "Bismillah, ko mu karasa mu zauna?" Ya fada a tausashe yana jan hannun RAUDA ya nufi kujerar ta Baki bude Amnah na kallonsa ta ce" Sir, wai me yake faruwa? Ni du kaina ya shiga duhu menene zai hadaku hadi irin wannan bayan abinda nake kyautata zaton Ni da nake uwar gida ba'a sauke min shi ba bale wannan ? Bayan wannan sirri ne fa, sirrina ne zan yi a gaban wannan munafukar anamimiyar da bata da mutunci?" Ido Rauda ta sake lumshewa a nutse ta kawar da kanta kasa kasa ta ce" Kar ka ja min zagi mana mijin Amnah, sakeni in tafi Please" Kallonta ya yi yana jin tamkar zai rasa nutsuwarsa ta kamewar da yake ta yi dan gudun ya yi abinda za'ace bai kyauta ba, sai ya ji haushinta da tace wai wani wai mijin Amnah, wai shine mijin Amnar? ita wannan ficiciyar y'ar me yasa ta iya neman balaki ne? me yasa take da son a yi balaki ne ? in ba dan gudun a fita ace ba alkur'an yau da ya basu fili sun yi idan suka gama ita kuwa wannan ya hade hannayenta ya yi mata hagu da dama da tsintsiya kwaya dari a kafta kaftan abubuwan nan nata na baya cikin nutsuwa da kwonciyar hankali dan ya koya mata kiyaye harshenta a kansa, mtssss kai kai kai! Mikewa ta yi itama ta sake shaƙar wani haushin, gannin wulakancin ya yi yawa, a zo har dakinta a raina mata hankali kuma ya kasa yiwa matarsa fada? lallema dan ta yi shiru ne za'a nemi a wulakantata?, rai bace ta nufi inda Amnah ke tsaye ita kuwa tana gannin ta nufota ta zabura da sauri ta bi ta dayan hannun ta nufi inda yake zaune tana fadin" Walahi kika saki kika kuma taba min jikina sai na kai kararki mai fadan mahaukata kawai, yaushe rabon duniya da hadewar jiki dan an gaya maka magana? ki rama mana baki da baki ne sai dai ki taba min jiki?" RAUDA ta dake kugu tana kallonta ta ce" Kin ga, ki tafin min a nan kawai, ko menene ai ke kika zo inda nake kike zagina, ki fitar min ko idona ya rufe na maki dukan mutuwa dan ba tsoronki nake ji ba, fita kawai" Murmushi yake yi a bayane saboda yadda Amnah ta bazo da gudu ta zo wajensa ta tsaya din nan da abinda ta fada da wanda RAUDA ta fada matan, ama taurin kai irin na Amnah sai ta ja tsaki tana fadin" Ni ai na ga tsoron naki nake ji, sai ki min dukan tunda uwata ce ke, ina nan din gidan mijina ne inada damar zuwa inda na so a lokacin da na so in yi abinda na so" RAUDA ta gyada kai tana kallonta ta ce" Ko? ok ina zuwa!" Ta yi ciki da gudu tana cire hijabinta ta nufi wajen wayar cazar computarta ta wartota ta cire dayan kan ta bar mai daɗin dukan ta bude wajen kayanta ta warto dogon wando ta saka ta saki zanin nata sannan ta dawo a haukace tana fadin" Bari in nuna maki ban haife ki ba ama zan baki tarbiyya!" Ganninsa zaune ya gyara zama ya tamabe haba ya saka RAUDA hadiye sauran zancen tana leke leke daga inda take kasa kasa ta ce" Ina take?" Haba ya sake rikewa yana kallonta, alkur'an bulala ce ta dauko zata zane y'ar mutane, wayo ya bani lamarinta karra daukaka yake yi, yanzu wannan y'ar haka take da rikici? "Tana inda kika ajiyeta, ke koma min ciki ko in zo in mayar da ke!" Ya bata amsa yana mikewa tsaye Da sauri ta bi tsayinsa da kallo ta juya tana fadin" Taraya zaku min?" Ya bi bayanta hakan ya sa ta afka dakin a guje tana kiran Mah Murmushi kawai ya yi yana girgiza kai ya fice ya nufi bangaren Amnah yana hana kansa fashewa da dariya, domin RAUDA na yin dakinta ita kuwa ta yi waje da gudu tana fadin tana dakinta dan Allah ya sameta zasu yi magana Da ya kwonkwasa sai da ta leko ta kofar lekawa sannan ta bude masa tana sake sauke ajiyar zuciya ta ja baya, yana shiga ta rufe ta datse tana sake rintse ido dan walahi ba zata taba yarda jikinta ya hadu da na mahaukaciyar matarsa ba tana kallonsa ta ce" Honorable yanzu fisabililahi kana kallo matarka zata ringa dukana ama ba zaka dauki kwakwaran mataki a kanta ba sai ta min lahani?" YUSUF ya yi tsaye kikam, bai yi alamun zai karasa ya zauna Bama a kujerun wajen, kai irin kwallon da yake dan bin dakin da shi zaka gane ba zai taba zama a cikinsa ba, a nutse ya ce" Kin san bata son zage zagen nan, idan kika kiyaye fa babu abinda zata maki" Tana cikin wani yannayi ne, kana ganninta zaka ga rashin nutsuwa a tatare da ita, abubuwa ne sun yi mata yawa, a yanzu haka ta nuna masa wajen zama ya kai sau uku yana dan sharewa, dan haka ta ringa yawo shi kuwa yana bin kaffafuwanta da kallo , a birkice ta ce " Sai ta ringa wani isa da isa kamar wace ka fara kwana a dakinta, Ni ai Ni ce matarka ta farko, Yaushema ya zo nan din? Ni ai bata isa ta gwada min sonka ba ai ka sani sarai fisabililahi ko?" Kai ya karra sokewa sai kuma ya dago ya dubeta, a cikin makogwaronsa ya furta" Uhum" Sai kuma ya ce" Menene maganar da kika ce zamu yi?" Sai a lokacin ta dan dafe goshinta ta furta" Au, wai su Mom ne suka yi kirana an kawo masu samaci daga gidan polisawa, shine nace kar su je bari in sanar maka yanzu yanzu a yi kiransa ya soke koma meye!" Cike da tausayin kansa da kansa da kuma karra tsoron lamarin nan yana dubanta da mamakin tun dazu samacin har ya kai masu, ta zo da nufin yin maganar ama ta bige da sanyo nata maganar , maganar banza maganar shirme, iyayenta jama'a? subahanallah subahanallah, shine bambancin haihuwar da Allah ya umarcemu mu yi, da irin wannan haihuwar Yana dubanta ya ce" A kan me zan saka ya janye maganar? a kan wani dalili aka kai masu samacin" Itama sai ta tsaya da yawon da take yi ta ce" Naga ai Ni matarka ce, zubar maka da mutunci za'a yi idan aka kai iyayena wai gidan polisawa, ban san dai abinda ake tuhumarsu da shi ba, ama ko menene karya ake yi masu !" Kai ya kawai saboda ƙarara shirmenta da haukanta yake gani a bayyane ya juya yana fadin" Idan sun kira , ki sanar masu su je din shi yafi alkhairi, dan ba zan hanna a tuhumesu ba idan sun yi laifi ko su wanene su!" Daga haka ya fice a dakin ya nufi nasa dakin, cikin nutsuwa ya shiga kimtsawa domin ga dukkan alamu fitar zata kama shi dole Ita kuwa ta jima a tsaye cike da mamaki da tsoron furucinsa, sai yanzuma wasu abubuwa suka ringa dawo mata da kamar ya ringa kaucewa ko ya fada mata gwa da gwa kukan wayarta ya sa ta karasa jiki a mace ta daga ta amsa kiran yayarta dake wani irin kuka tana fadin" Ke wai kina gidan uban waye wai? yanzu su Mum na waya da lauyansu yan gidan su kawar nan Tata da suka yi fada ta baya suka shigo har ana ririkesu sai sai sun kasheta da hannayensu, wai samacin da aka kai sunne suka kai, wanda ya zo din ya'yan wannan y'ar Tata ce da ta rasu wai walahi ba zai yi jiran hukuma ba da kansa zai daukarwa kansa fansa, wai mum ta saka laya a bakin kanwarsa aka binne ta da ita, wai yau itama sai ya dinka mata layar a baki, da kyar masu gadi suka fitar da shi anguwar nan an zagayeta an cikata da samari dai jifan gidan nan suke sai da dad ya sa aka kawo sojawa, yanzu hanyar da zamu bi mu fitoma ta gagara, innalilahi ki gayawa mijinki kin san yaransa ne idan ya yi magana sunna ji ama kina cen kina hutawarki!" Wani irin ihu ta saki tana zaro idannuwa, dan adu'ar da zata yi ta nema ta rasa a bakinta , A rikice ta ringa rarumar hijabi tana fadin" Bari in sanar masa, ina zuwa, ganinan Ni dinma , laya kuma? a bakin mataciya? wace laya ce kuma mun shiga uku, laya? laya?" Ta fito da wayar a hannu ta yi niyar nufar bangarensa ta jin kanshin turare ya gama cika falon baba gaba daya, sai kuma ta ji karar bude kofar baya ta bangaren da yake ajiye da yan kaso Da sauri ya nufi wajen, dan bata tunanin zata iya jiran dawowarsa ko ina zai je "Sir, Sir" Ta fada da dan karfi, Da sauri Taj ya yi baya ya tsaya , shi kuwa ya ja ya tsaya har ta karaso jikinta na rawa ta shiga fada masa lalle lalle zata je gidansu ba lafiya kuma ya taimaka mata ya tura wani a yiwa samarin anguwarsu tsawa sunna son kawo raini gidansu Ajiyar zuciya ya sauke yana dubanta, a tausashe ya ce" Amnah, ki nutsu, ki fuskanci komai a nutse yadda ba zai ji maki wani ilar ba, babu wanda zai shiga gidanku ba za'a bari kowa ya tarda mahaifiyarki ba, ki kula, idan kika dauki abin ta wata fuskar tabas zaki lalata goma biyarma bata gyaru ba, baban abu ne ya tunkaro ki, in kika yi wasa da ganganci zai cin maki, maganar laya gaskiya ne ta aikata, za'a gurfanar da ita, idan kin san kina ciki ki shirya dan babu wanda zan kyale , Amnah ki nutsu kar ki janyowa kanki idannuwa a lokacin da kurarki zata yi kuka, ki guji baki, shine kawai abinda zan iya fada maki" Daga nan ya juya ya fita Taj ya maro kofar ya saka mata sakata A tsaye take a daskare tamkar ta summa, da kyar ta iya tuna abinda ya fada ta maimaitawa kanta, hakan ya sa a rikice ta zarro ido ta kama kofar ta ja ta ja ta kasa budewa da gudu ta juya ta nufi dayar kofar itama ta kama ta ja ta ja ta gaza budewa, ashe nan din ya fara bada umarnin a garkame kafin inda ya bi, A haukace ta zube ta tartsatsa wani irin ihun da ya sa RAUDA mikewa a zabure ta nufo falon tana ajiye wayarta da suke yi ita da ATU tana sanar mata zuwan Mama hudu tana sake yi mata magiyar dan Allah ta yi mata hanyar da zata ga RAUDA din, mama ciwo ya cita ya gama cinyewa, bata da lafiya kuma tace wai a asibiti ance ba'a ga komai ba, gidan haya an koresu saboda a bayane Salaha ke kawo maza tana lalatarta, karshe salahar yanzu bata san ina ta shiga ba, ita kuma sai dai ta kwana a inda dare ya kamata idan safiya ta yi ta ci gaba da bata, aikin aikatau ya gagareta samu duk inda taje kyankyaminta ake yi ana yi mata korar kare, harda wajen da aka yi mata lakabin marainiya daga zuwa neman taimako, wannan lamari na shiga kunnenta a kwoncen nan ne ta ji ihun nan na RAUDA Da sauri ta karaso tana kallonta , da kula ta shiga kokarin kamata tana fadin" Subahanallah, lafiya? menene? ke? menene?" RAUDA ta kasa daina ihu da burgima, a bayane kuwa fadi take yi " azl65 *MAGANIN KARA KIBA 3IN1* *Ina meneman kiba ido rufe Kuma tanason maganine ingantacce Wanda baida illah kokadan to tazo gadama tasamu yar uwa indai kibace da gyaran nono dakara hips toga Mganinmu nan 3in1 cikin kwana 7 kacal👌🏻 zakiga yadda Zaki fara murmurewa insha Allah mungwada mungani munbayar angwada munsayar angode insha Allah kawata Zaki godemin da 3500 dinki kinhuta da gorin rashin kiba munan cikin Gombe Kuma munatura kaya ko ina kedai tuntumebi ta Whatsapp ko kikirani Kai tsaye ta 08030861857 sai kunzo🥰* *MAGANIN HIPS* *Wannan Maganin anyisane tamasu neman hips sunsha wannan sunsha wannan to gatamunan insha Allah guarantee nakebaki hajiya inada yakini akanta matsala indai tarashin hips ne to anwuce gun 3500 kacal kinhuta kijuya kiwarwasa kisaka kayan gayu kijuyawa Oga yayikallo kawata har yanga saikinmasa ninafadamiki wannan nemeni kisamu naki 08030861857* *MAGANIN NONO* *Itama akwaita me inganci kamarta 3in1 data hips wasu suna korafi nifa nono kawai nakeso yaciko yayi bulbul gwanin sha'awa yadda Oga zaiyaba nasa breast cup suzauna das Amman abun yacitura Nasha Nasha magungunan Amman haryau ba chanji to ganamu Nan yakine ne Dani akansa ba Dan kadanba alhamdullahi duk Wanda yasaya saidai godiyace tsakaninmu kema zokigwada Kuma kigodemin location Gombe 08030861857* A rikice take fadin" Na shiga uku, na shiga uku, wayo Allahna waye ya fada masa, wayo na shiga uku waye ya fada masa? kar dai saboda wannan abin a kashe min aure, kar a hadani da mijina a rabani da gidana, sun rufe sun hannani fita gashi ina kiran maman dan in fada mata bana samu, wayo Allahna!" Ihu take yi tun karfinta da kuka, du yadda RAUDA ta so kamata ta gaza, hankalinta ya tashi ainun, domin abinda Amnah ke yi ba wai abin wasa bane, dole mutun zai tausaya mata, Da sauri ta je dakinta ta dauki wayarta ta shiga ta nemi layinsa dan ya mata salamar ya fita ta waya, ta shiga bugawa, ama ba'a dagawa, a dole ta nemi layin Mah dan har yanzu ihun Amnah bai rage ba, tamkar wace aka cewa iyayenta sun rasu? subahanallah hankali tashe ta shiga sanarwa Mah abinda ake ciki Mah dinma muryarta a dan birkice ta ce" Baby, ki zauna a dakinki za'a zo a rako ki, itama za'a kawota kar ki damu ba komai bane in sha Allah" Mintunna ƙalilan Jakadiya baba ta zo ta baya aka bude mata bisa umarnin Mah ita da wasu ma'aikatan bangaren Hajia baba suka tafi da Amnah dake cikin halin fitar hayaci, domin ta daga kiran yayarta ta sake daga mata hankali itama ta sanar mata abinda yake faruwa ta dora da fada mata wace gawa ce Mamansu ta sakawa magani?, har abin ya zo kunnen MALEEK?, baban tsoronta da firgicinta Sannin waye MALEEK, domin koda basu zauna zaman aure na mata da miji normal ba ta ji waye shi ji na gasken gaske ba jin hasashe ba, kuma ta ga wasu aiyukan a aikace, itafa tunda aka fada mata marisha babu irin haukan da bata yi ba a kan MALEEK tun yana matashin dan kasuwa ta ji ta sake riƙe shi a zuciyarta, domin marisha din nan babar mai kudi ce dake zaune a baban birnin Nijar wace ke cikin gwamnati kuma take tare da manyan kasa, wace ta san ta dame babansu ta shanye a kudi bale wai su, ta ji lalle ta kai , tunda yau za'a dubeta ace itace matarsa?, idan har aka rabata da shi bata tunanin in zata iya rayuwa, ta sanarwa yayarta ko me Mamansu ke yi na asiri sai ta fada sannan ta nemi ita a cireta a cikin rikicin nan dan walahi ba zata yi saken rasa MALEEK ba! Ita din suka fara kaiwa, sannan suka dawo Jakadiya ta raka RAUDA har wajen Mah dake daya daga cikin dakunan bangaren Hajia tana kwonce dan saboda yannayin jikinta Amnah kuwa a dakin Hajia aka sauketa, cikin ikon Allah tun kafin Hajia ta nemi Sannin wani dogon bayani a wajenta ta ringa tona mata sirin mahaifiyarta har sai da abin ya gigita Hajia, domin bata taba tunanin rayuwa na iya kasancewa haka ba, a dole ya nemi sheda a kusanta da kuma wanda zai zamo wanda zai yi magana da Amnah, dan ita yarinyar ta fara bata tsoro, irinsune ke shiga haukan karfi da yaji idan suka rasa wani abin da suke so, shi yasa ta fito ta yi jiran zuwan Bah wanda ya baro wani rikicin a babar fada da ake tafkawa da jama'ar gari kan a basu mahaifiyar Rauda su konata da ranta, domin irinsu barin su a doron kasa tamkar busa guba ne a cikin iska, sai dai du abinsu basu iya shiga baban dakin taron da ake ta dauki ba dadi da mahaifin Amnah wanda ya summe tunda aka kona layar da aka ciro du ta yi hijoji cikin tsuma ya kai biyar, sai dai layar na nan bata lalace ba, shi yasa baban malamin masallacin Masarautar ya sa aka hada garwashi yana ta adu'a ya kona layar da hannayensa, sai ga mahaifin Amnah dake rikicin karya ake yiwa matarsa shari ne ya fadi kasa sumame , da kyar aka samu numfashinsa ya dawo jikinsa, sai dai yana ta wasu irin abubuwa kafin a samu ya yi wani irin tashin da aka hanna shi mikewa tsaye cirr bisa umarnin malan, ana ta masa karatu, malamai zagaye da shi, YUSUF na zaune saman kujerarsa ta mulki, sojawan da suka kamo su maman Amnah na zazaune kowa yana jiran wannan abin da akace a fara warwarewa kafin a hau shara'ar Cikin ikon Allah ya dawo hayacinsa, cikin wani irin yannayi ya ringa bin mutanen wajen da kallo, hankalinsa na neman sake dugunzuma ya tashi, du kamar wanda bai sansu ba bai taba Sannin kowa ba, bakinsa na buduwa a rikice mahaifiyarsa ya fara tambaya sai matarsa auwar gidansa Tun da mahaifiyar Amnah ta ga haka ta nemi zubewa, aka nuna mata ba dama domin kiri kiri ana nuna mata ko gawarta ta shiga uku bale ita, a dole ta ringa rusa kuka a zaune hannayenta saman kanta tana fadin ta shiga uku, karshe dogari ya tsawatar mata cewar ta masu shiru a gaba dai zata shiga ukun Tun daga lokacin tone tonen abubuwan da ta aikata suke bayyana a hankali har zuwa kan maganar ya'yan da ta haifa da shi su biyu yan mata, ta tabatar da ba nasa bane na abokinsa ne, wanda hakan ya sake rikita mutanen wajen da tashin hankali da Allah wadai da suke yiwa abokin nasa, shi kuwa zuwa lokacin ba baka sai ido, domin abin ya gama tsoratar da shi, ya zamo harta dukiyar da ta janyo masa kuda tamkar sun ga zuma ta shiga bashi tsoro hannayensa cikin na Mahaifiyarsa, matarsa uwar gidansa a gefensa zuciyarsa na karra karyewa irin yadda shi mutun mai zumunci, mai kiyaye dokokin Allah da hidimtawa addinin musulunci ya samo shi ba kafuri ba shi ba Musulmi ba yana rayuwa da makiyansa a gefensa, su basu kashe shi ba, su basu barshi ya rayu ba hukunci aka yanke masu mai tsanani ita da abokin aikata masha'ar Tata, da kyar polisawa da dogarai suka tare mutane aka samu aka fita da su aka tafi da su , hakan ya sa rikici sake balewa sunna nuna a basu su su koyawa masu irin halayarsu hankali, sai da MALEEK ya fito da kansa ya yi tsayuwar sarki a gaban su, tsayuwar ja gaba a gaban su, tsayuwar malamin su, tsayuwar uban gidansu idan fannin a fito na fito din, sannan tsayuwar aboki a gaban su, cikin Yaren da zasu fi ganewa na nasiha da kuma tsauri ya tsawatar sannan ya bada umarnin a yi hakuri a koma gida, mai aikin yi ya koma bakin aikinsa, hukunci ba a hannayensu yake ba, an riga da an yanke masu hukuncin da sarki yake da ikon yankewa, sauran zancen yana kotu domin iyayen marigayiyar idan sun daukaka kara sai a je a kalli Shari'a, sannan ya rufe taron da kakausan kashedi da alkawarin yankewa duk wani wanda ya taka doka hukunci in dai a cikin garin TSATSUNBURUM yake! Dan karamin hauka Amnah ta tadawa su Bah bayan duk irin nasihar da ya yi mata da tausarta da nuna mata irin kular da za'a basu ita da yayarta da kuma inda za'a tura su rayuwa duk dan ya tabatar mata a yanzu ba zata kuma amsa sunnan mata a wajen MALEEK ba, sai dai ta yi hakuri Allah ya bata malamuncinta tabas su zasu daura mata aure idan wani ya fito mata Da kyar suka samu abin ya koma rizgar kuka kawai da cimuimuyar hijab da tarin tashin hankali marar misaltawa a lokacin da ta samu yayarta itama ba yadda take suka ji tamkar ace basa raye a duniya da wannan tashin hankali, gashi sunna ji sunna gani a cikin gidan mahaifin da a da suka fi kowa isa da tunkaho a yanzu sun boye sun rasa inda zasu saka ransu domin uban da suke takama da shi aure ne ya bashi ama ba nasa bane, kuma ya nuna idan sun so zama ba zai hanna ba, sai dai shi kam bai san wani irin zama zai yi da su din ba, abinda ya sani kawai zai kiyaye hakinsu a kansa, shi yasa shi dinma ya fi yarda da maganar fitarsu daga garin, domin ya riga ya san cewar a yanzu zaman garin nan ya fi karfinsu, rayuwar da suka yi a da tamkar su suka haifi kansu a yanzu ba zai taba iya zuba masu ido su maimaita ba , dan haka duk inda za'a kai su zai yi iya yinsa dan gannin ya fita hakinsu, wannan tashin hankali ya karra saka Amnah a mummunan halin da ya nemi jirga tunaninta, ba ruwanta da halin da mahaifiyarta ke ciki, domin ba itace a gabanta ba, abinda ya fi rikitata damuwarta da asarar da ta gane cewar ta tafka ta rayuwa fiye da komai, asara ta duniya da kiyama idan bata tuba ta koma ga Allah ba, ba mutunci, ba usuli, ba MALEEK, kadararta mai zafi ce wace ta hannata sukuni sai kuka da maimaita kalaman mahaifiyarsu ta cuce su da ta bi wani mutumen har suke hayayafa da aurenta, fadi take yi ita ta san ba zata rayu ba ba MALEEK........ (Allah ka hanne mu aikata aikin dana sani, ka rabamu da muguwar Kadara) Sai bayan isha RAUDA ta koma bangarenta bisa rakiyar Jakadiya, wace ta yarda ta tafi da kyar bayan Mah ta tabatar mata jikinta da sauki suka shigo har baban falon daga nan Jakadiya ta duka cike da girmamawa ta yi mata salama, ita kuwa ta rasa yaya zata yi dan gaba daya yanzun sai take jin bangaren ya yi mata wani irin girma, a dole ta lalubo wayarta ta dannawa salima kira suka shiga dan zantawa tana yi mata nacin ta zo bangarensu, ita kuwa tana fadin wane ita, ba yanzu ba, Bah ya masu kwakwaran kashedi cewar ba yanzu ba, karshema firar ta ki dadi dan Rauda ta rasa yaya zata yi da ita kan dan Allah ta zo ita gidan ya mata girma, a dole suka yi salama ta sake dokawa Atu kira, ama take ringin ba'a daga ba sai a kira na biyu ne Atun ta daga kamar wace ke barci ta ce" Sweetheart " A hankali, cikin yannayin sanyin jiki da Muryar da ta wuni da shi ta furta" Atu, kin yi barci ne?" Atu ta sake bude idannuwanta da kyau ta ce" Ina kwoncen dai, yannayin nan na saka kasala sosai, yaya kike, lafiya nake jin muryarki wata iri?" RAUDA ta sauke ajiyar zuciya a hankali ta ce" Atu , Bana tunanin zan iya, karfina karewa yake kokarin yi....., Atu ke kin san burin irin mijin da nakeda a rayuwa, Atu sarauta ba tawa bace, gaba daya rikicinta da irin yadda na shigota nema suke yi su karar da karfina " Da kyau Atu ta zauna tana sauraron Rauda, ta bata dukkan kulawarta saboda ta sani idan har Rauda ta budi baki ta fara magana haka tana cikin babar damuwa a zuciyarta a tausashe ta ce" Subahanallah, wani irin ba zaki iya ba? me yake faruwa? wani abin yayan ya maki?" RAUDA ta lumshe idannuwanta tana jin irin yadda take son yin maganar kamar ba za'a fahimta ba A hankali ta ce" Babu abinda ya min, Ni dai nake tsoron kasa zamowa abinda nake son zama, " "Tl me, me yake damun ki, Please ki min magana dala dala mana " Atu ta fada a tausashe dan zata so ace RAUDAR ta yi kokari sun yi maganar yadda ya kamata saboda ta cire mata damuwarta Huci Rauda ta fitar mai dan dumi a hankali ta ce" Na riga na yi saken da kadarar zuciyata ta cafki wanda ya zamo gogage a lamarin kwaliyar mace da duk wani abin da take iya birgeshi da shi, uwa uba yake da ya'yan banki , da kuma RAWANI Atu...." Ta ajiye tana lumshe idannuwanta dan jin nauyin abin sosai a zuciyarta da harshenta A hankali ta ɗora da fadin" Dan son kai irin nawa, nake jin haushinsa da matarsa bayan na san wanda aka aura min ko bayan mata idan yana da bukata zai iya ajiye kwarkwaraye su amsa kiransa a duk lokacin da ya so...., Atu tana iya kasancewa ganninsa ya min wahala a lokacin da na so, kuma magana da shi ta zamo aiki a lokacin da na buƙata,......Atu ina tsananin kishinsa wanda ke neman yi min ila , bayan na san wa nake aure....uwa uba na fara shakun in har zan iya birge shi ko na ga abinda nake son gani da ji ƙarara ba ta wani yannayin da nake jin ana iya ba wata dina ba!, Atu ban san yaya zan kwatanta maki ba, ina iya cewa ina jin kaina tamkar ba mace ba a gabansa........duba ki gani yau kwana na na h..........." Dif ta dauke maganar sakamakon bude kofar nan ta baya ta wajen hanyarsa ta sirri da aka yi aka shigo A hankali numfashinta ya shiga sauka daya bayan daya sakamon gannin bayanuwarsa a cikin idannuwanta a irin wannan lokacin da ya shigo yannayinsa a gajiye, sai dai daga tafiyarsa ba zaka gane ba sai ta idannuwansa da suka yi wani irin lumtu, shigar jikinsa kuwa banda daukan ido da shiga ido babu abinda take yi, domin ta hau jikinsa das ta zauna Bama kamar alkyabar dake jikinsa A hankali wayar dake hannunta ke neman subucewa, duk bayanan da Atu ke kwararowa ta daina fahimta har sai da Atun ta dawo maimaita hello hello ama tamkar ba kowa a wajen, bayan ga call din bai mutu ba kuma takan ji abin Ac dake dan tite tite lokaci zuwa lokaci wanda ke tabatar mata ba network ya datse kiran ba Idannuwansa a kan fuskarta suke, tunda ya shigo din Gaba daya fuskar yake kallo da zagayayen hijab dinta wanda ya matukar bi kyan fuskarta ya kawatata.....shi fa a da yana yiwa hijab kallon abinda in za'a yi sallah ya dace a ringa sakawa dan a ganninsa in rufar ce ai abayama sutura ce, sai dai tunda ya santa ya ringa ji a ransa idan zai samu ta ji komin girman suturar da zata saka ta dora baban hijab da nikab, zata fi kyau a haka......... Idannuwanta ta sauke saboda dokawar da kirjinta ke yi, cikin yannayin sanyin nan ta dan dago zata kuma kallonsa da sauri ta lumshe idannuwanta sakamakon maganar da ya fada dazu da safe kafin matarsa ta katse su, wata irin kunya ta ji tana neman rufeta a zaunen da take dan haka ta kai hannunta a hankali ta shiga dan murza goshinta sannan ta dago muryarta a boye sosai, sai dai amon na shiga kunnayensa ta furta" Barka da shigowa" Idannuwansa ya lumshe a hankali ya karaso inda take zaunen yana Binta da kallo, wayarta da ta saki jikinta ya saka hannu a hankali ya juyo da ita ya ga kira na tafiya da kuma sunnan ATU Numfashi ya fitar kadan, kasa kasa ya ce" How Are You?" Da sauri Atu ta datse kiran tana talabe kuncinta a ranta tana ayana' Dama yana nan take waya da Ni a irin lokacin nan?, wai wani ba zata iya ba, Ni na yarda ki Kunno fitinar da zata sa ki haukace min a nan ke daya ki ringa fada ? ke da MALEEK daidai da junna ne, kuma ke ce mahadinsa' RAUDA kam kasa sake bude baki ta yi a lokacin da ya kai bayan hannunsa dake fitar da kanshin turaransa mai naci ya dan shafi gefen fuskarta ya bar hannun a jikin gefen fuskar nata bayan ya dan duko da tsayinsa kadan Dayan hannun nasa ya saka yana dubanta a nutse ya kama hannunta na dama da dayan kuwa ya talabi gefenta ya mikar da ita tsaye yana kallonta kasa kasa ya ce" Menene?" 66 A hankali RAUDA ta saukar da dubanta daga cikin nasa muryarta cen ciki ta furta" Ba komai " Dan murmushi ya yi a nutse ya furta" zan samu tea dina? za'a bani yau?" dagowa ta yi a dole ta dube shi tana jin murmushi na son maye gurbin tashin hankalin da take ciki, dukda ta gama kwanakin da ake yiwa amarya bazawara irinta tun jiya, ba zata ki kai masa tea dinsa ba, bata jin zata taba iya kasa amsa bukatarsa a rayuwa ta wani aikin da zai iya sakata, dan haka da dan murmushi ta gyada kanta shi kuwa ya furta" Thank you" Sannan ya saketa ya nufi Part dinsa yana sauke alkyabar jikinsa tun a hanya yana sake sauke rawanin jikinsa dan abinda zai fara yi a yau shine shiga ruwa masu zafin gaske sannan ya samu hutu mai kyau ko zai dawo daidai Yana shiga dakin kiran ISHAK na karra shigowa wayarsa Dagawa ya yi ya masa shiru bai ce komai ba ISHAK ya sauke ajiyar zuciya muryarsa dake cikin halin karaya kusan sati guda cirrrr a wannan yannayi ya ce" Barka da warhaka Sir" YUSUF ya yi shiru na yan dakiku sannan ya dan sauke numfashin dake tabatarwa ISHAK yana jinsa ISHAK ya sake shan jinnin jikinsa, gaba daya so Yusuf yake ya birkita masa lissafi, tsoronsa daya kar aje YUSUF ya dan abinda ya sa ya shiga jikinsa? Sai dai wata zuciyar na fada masa kai ina da ace ya sani ne da tuni ya nemo shi in a ina yake ya wanke masa dukan rashin tarbiyarsa, ya fi kyautata zaton wani abin ya masa a rashin sani ya sa yake share shi A tausashe ya ce" Sir, dan Allah idan wani laifi na yi ka yi hakuri ka yafe min, na kasa gane dalilin da yasa ake hannani zuwa inda kake bayan kaf cikinsu babu wanda bai san tskaanina da kai ba, ya zamanto Taj har hannani zuwa gidanka na cikin gari ya yi, dan Allah ka yi hakuri" Yusuf Ya idasa cire babar rigar da ya wuni da ita yana jin da wahala kuma ya iya mayar da ita jikinsa dan yau an sha gumurtu da ita, a nutse ya ce" Ka san dare ya yi yanzu, kuma inada iyali, zan tabo ka" Daga haka ya katse kiran ya idasa tubewa ya bar gajeran wando a jikinsa sannan ya nufi bayi da takalmin wankansa ya shige a zuciyarsa ya gama sakawa ransa tabas zai yafewa ISHAK a ci gaba da zaman tare ama idan shima ya daina halayan da suka hadasu abota, sai dai zai yi zama da shi na zumunci ne kawai, daga wannan baya tunanin akoy kari dan a zuciyarsa ya riga ya kamu da tsarguwa da lamarinsa RAUDA na shiga kicin dinta ta kunna fitilun kicin din ta shiga nazarin abinda zata dora A dole ta karasa wajen wayar dake jikin bango ta daga ta yi kiran bangaren masu aiki Wayar na daukan ringin aka daga da salama A nutse ta amsa sannan ta furta" A turon mutun daya kicin " Da sauri chef din kicin din ta amsa da " Yanzu kuwa ranki ya dade" Sannan ta ajiye kiran ta taso ta taho da kanta saboda aikin uwar gidansu ne baki daya Tana zuwa ta samu RAUDA har ta fitar da kayan aiki, ta fara wa'inda zata fara dan ta gama da gagawa da girmamawa ta gaisheta , itama ta amsa da kula sosai da kuma ba chef din girma ko dan finta da ta yi a shekaru da kuma sabon da ya shiga tsakaninsu, dan tunda aka kawo RAUDA kulun tare suke yin girki, gaba daya firarta suke yi idan suka zauna da fatan Allah ya sa ita din ba kamar Amnah bace, domin Amnah suma bata masu da sauki ba, sak ta nuna masu bayi suke bauta zasu yi mata,kuma ba ruwanta takan shigo a lokacin da mazan nan suke ta sa a yi mata girki , har ta taɓa nuna ita ta fi son abincinsu fiye da na matan cike da gadara da kaskanci take masu magana koda aiki take son saka su, RAUDA kuwa aikin girkin gaba daya da ita ake yi, cikin mutunta junna da girmama junna tamkar ba itace matar MALEEK ba Abubuwan da take buƙatar a yi mata ta nunawa chef din sannan ta ci gaba da aikin Nan da nan suka gama girkin abincin kala daya mai sauki sannan ta haɗa drinks na lemun aya da kankana ta kilace komai ta kuma hada kayan tea din nasa da kula ta ce da chef" Ina zuwa Chef " Chef ta dan dukar da kai ta ce" A fito lafiya Gimbiya" Ita dai Rauda bata kuma cewa komai ba ta nufi dakinta tana jin ba zata iya kai abincin ba tare da ta dan watsa ba, rabonta da wanka fa yau tunda safe, gaba ɗaya ita bata san abinda yake faruwa ba, ta wuni gefen Mah ne dake fama da jikinta dan kaffafuwanta dake ciwo, sai Hajia dake kiran Mah din lokaci zuwa lokaci ta je ta dawo, ta tabata a kan wannan ihun da Amnah ta ringa yi ne, ko me yake damunta da zafi haka? gaba daya Amnah lamarinta a rikice yake sai adu'a Wanka ta yi ta fito jikinta na digar ruwa ta dauki tufafinta riga da dogon wando na barci mararsa nauyi ta saka sai turare da ta shafa a duk wani lungu da sako na jikinta dan ko mai bata shafa ba, so take yi daga ta kai masa ta dawo ta samu ta kwonta ko zata samu yin barcin ranar da bata yi ba yau, sai a lokacin ta turawa Atu mesg cewar zasu yi magana gobe in sha Allah A nutse ta dawo kicin din ta tararda chef ta haɗa mata komai a saman baban faranti mai ruwan zeba mai nauyi sai Khali yake, kayan kuwa sun jeru masha ALLAH harda tea din, ta rike da kyau tana yiwa chef din godiya, ita kuwa tana sake tambayar zata iya kuwa? har sai da ta ga ficewarta sannan ta sake kashe komai na kicin din ta kulle da ky din kicin din ta fice ta baya ta kulle ta koma bangarensu na masu aiki , domin dama dokar bangarensa da zarar sun gama aikace aikace suke tafiya nasu bangaren, sai manyan dake kula da wajen ne ke zuwa lokaci zuwa lokaci su saka turare su karra kakabe kakabe koda kuwa babu wanda ya fito, sai ko idan an yi kiransu dan wata bukatar kamar yadda RAUDA ta yi kiransu yanzu, dokokin YUSUF ne Wadinnan , Hajia sai da ta nuna hakan ba zai gyara matan gidan ba ya nuna shi haka yake so, yana son bangarensa ya zamo wajen sakewarsa ba wajen buyansa ba! A nutse take knowking a kofar dakin bayan ta ajiye kayan, domin ba zata iya bugawar da kayan a hannayenta ba, idannuwanta kuwa babu abinda suke yi mata sai yaji yaji da muradin sake kallonsa da wannan salo nasa kafin su kwonta A nutse ya bude kofar, da waya a kange a kunnensa yana amsawa ya sauke dubansa a kan fuskarta Dauke nata duban ta yi ta duka ta dauki kayan abincin ta dan raba shi ta shige ta nufi wajen ajiyewa ta ajiye sannan ta juyo dan komawa idannuwanta suka sauka a kan ky din hannunsa ya nufi wajen wrdrb din nan ya kuma ajiye shi a inda ta yi ta dage ta kasa daukowa hankali kwonce yana waya kan harkar kasuwancinsa A wajen da take tsaye ta kasa motsawa ya waigo ya kalla, da hannunsa ya mata nuni da wajen zama, wato wajen kujerun nan da ta ajiye abincin Jiki ba karfi ta karasa wajen ta zauna tana dan murza hannayenta tana sauraron muryarsa, irin yadda yake magana da turanci tamkar a harshensa aka fara jiyowa, cike da classs da kwarewar harshe Kasa kasa take dan satar kallon afaffuwansa dake saman farin tiles din nan farare kar kar , a saman yatsutsan gashi ne kwonce lufluf haka kuma daga sama kadan kafin inda jalabiyar jikinsa ta rufe tana iya gannin duhun gashin dake kwonce lufluf a jikin kaffafuwansa, sai ta cire kai ta lumshe idannuwanta ita kadai tana tunanin rayuwa Ya jima yana wayar nan , har sai da ta gyara yannayin zamanta sannan ya katse ya kai wayar ya ajiye bayan ya kasheta domin baya son takura, sannan ya taho a nutse ya zauna saman kujerar nan zama irin na hamshakai wanda yake zamansa tun bai kai a kira shi namiji ba "Ina zaki tafi?" Ya fada a hankali yana dubanta Dagowa ta yi kan dole ta dan dube shi, a hankali ta ce" Dakina" "Kina da wani dakin ne sama da nan?" 'To ko ya manta mace biyu gare shi ne?' Rauda ke ayanawa a zuciyarta, a fili kuwa ta ce" Tun jiya na cika kwana ukun da ake yi fa" Shiru ne ya wanzu a wajen, ita tana jiran jin umarninsa dan ta kula karfinta babu abinda zai kwatar mata, shi kuwa yana tunanin lalle y'ar gidan Mah tana tare da neman masifa walahi, in ba wannan ba so take yi sai ta bata masa yannayi ne? ok kwana ukun da ake yiwa wace ta taɓa aure take son fada masa ko?, shi yasa ya yi shiru har sai da ya cire abin a ransa sannan ya ce" Srv me" Ajiyar zuciya ta sauke jin amon muryarsa dan har ta cire tsamani A nutse ta fara zuba masa abincin ta dora a karamin teburin ta matsa gabansa, sannan ta dauki sauran kayan bukatan duka ta kai gaban nasa ta ajiye tana kokarin komawa wajenta ta zubawa hannayensa ido da ya saka ya zaunar da ita daga da shi sannan ya saka cokalin a nutse ya fara cin abincin hannunsa daya riƙe da nata yana shaƙar kanshin turaran da ta yi anfani da shi, har ya gama ya sha ruwa kadan sannan ya sha tea din da guminsa sosai hakan ya sa ya sauke ajiyar zuciya yana jin nutsuwa na sauka a cikin jikinsa, dan rabonsa da abincin kirki tun jiya, yau din basu rigaya sun karya ba ya fitar nan sai dawowar nan da ya yi Dubansa ya maido kan RAUDA dake jira, a hankali ya ce" Cire hijabin mana ki sha iska" RAUDA ta yi raurau tana kallonsa ta ce" Ni da zan tafi yayanmu?" Murmushi ya yi ya mike tsaye , hannunta dake cikin nasa na cikin ya mikar da ita a hankali ya janyota jikinsa ya rungumeta, kasa kasa ya ce" Da na yi part part a nan, saboda kar y'ayana su ga ina kwana a dakin ki,........ama in dai ina nan kuma kina gefena cen ne makwoncin ki....... Bismillah" Jikinta karra mutuwa ya yi, a hankali ta dago dubanta ta sauke kan sagen fuskarsa da kanshin da jikinsa ke fitarwa, tana kallon nasa ya raba jikinsa da nata a hankali ya nufi bayi da nufin yin bruch Idannuwa ta rintse tana jin tamkar ba ita ba, 'Ya Allah, ina son bawan nan naka, ka sasauta min yadda nake jinsa a raina dan bana so hakan ya zamo min ila' Shine abinda ta yi ta ayanawa a ranta har ta ji motsin fitowa daga bayin, a hankali ta shiga tatare kayan abincin ta hade waje kuda a ranta tana ayana' Allah ya sa ba abinda zai ɓaci kafin safe' A nutse ta je ta zauna wajen kujerar dake daf da sif tana kokarin kin hada ido da shi domin ya gama ya je bakin gadon ya zauna ita yake kallo, a sanyaye ta ce" Yayanmu, dangane da maganar kwanan ne nace wai tun jiya ne na gama" "RAUDA zo mana, ko na zo ne?" Ya fada yana katse furucinta Gabanta ne ya fadi da ta sake dubansa, tsoro sai yanzu ya fara shigarta na wani abin daban, da gagawa ta cire abin a ranta dan sai ta tuna da ace zai yin da ya yi fa, kai da ace ma tana cikin layin wa'inda zai iya yiwa wannan duban ai da ya mata, hum, takaici ba zai daina kasheta ba a kan tunanin lamarinsa, dan haka ta mike din ta je din dan ta san idan ya zo din babu abinda zai rabata da shi sai Allah, tsaf zai iya yin du abinda ya yi niya! Murmushi ya yi bayan ta karaso ya kamata ya zaunar da ita saman gadon bayan ya kama hijab dinta ya cire shi gaba daya kanta na kasa tana dan murza hannayenta alamun jin kunyar kasancewa da shi a zaune waje daya a haka ya saka shi sakin murmushi, tabas kunyarta na matukar birge shi, da ace wata dinta ce ta gama wuce babin Hajia baba ai ba zancen jin kunyar namiji ko waye , ita kuwa masha ALLAH akoyta da jin kunya Gashin kanta yake ta kallo har zuwa wuyanta mai daukan ido da tsari kafin ya sake duban hannayenta fitilar gefen gadon ya kashe sannan ya kashe ta dakin da ta cika dakin a nutse ya janyota jikinsa suka kwonta ya zamo bayanta ke kirjinsa, shi yasa hancinsa ke shaƙar kanshin man gashinta yana kuma sauke mata numfashinsa a wuyanta wanda hakan ke hargitsa tunaninta dan ji take yi tamkar yana yi mata tafiyar tsutsa ne a sasan jikinta baki daya Idannuwanta lumshe suke nutsuwa na ratsa jikinta A hankali YUSUF ya ce" RAUDA?" RAUDA ta bude rinanun idannuwanta da suke cike da shauki ta dan jimke hannunsa dake cikin nata cen kasan makoshi ta amsa kiran nasa tana sake narkewa a kirjinsa A cikin makoshin shima ya furta" Ban yi zaton zan yafe maki ba, da kika auri wanina" Idannuwanta ta sake budewa a hankali tana jin kirjinta na dokawa, a hankali ya furta" But i cn............. i cn RAUDA..............i........i Da karfi ta juyo daga bashi bayan da ta yi ya zamo yanzu tana duban fuskarsa mai cike da girma da daraja da kuma wani irin fuzga wanda yake bayane a duniyarta, idannuwansa kuwa duban cikinsu ya nemi saka numfashinta daukewa, tana dubansa ya ce" Mah tace, ba lalle ne a so hada zuri'a da Ni ba, saboda babu abinda ban aikata ba na rashin ji.........tel me , zaki iya hada zuri'a da Ni RAUDA?, plz zaki iya rayuwa da Ni?" Kai innalilahi, haka Mah din ta fada masa? uhum Mah kennan, bata san rayuwar nan yadda ta zama ba? an so wanda ke cikin aikatawama bale wanda ya daina? an zauna da wanda zai aikata din ya nuna babu ubanda ya isa da shi bale wanda yana yi din yana kuma kiyaye wasu abubuwan.....kai Bama wannan ba, a rayuwar nan da ta zama kai sata Ni maita ai dole sai da taimakekeniya, Allah ya raya zuri'a kawai ama ai da wahala idan RAUDA naɗa wani mijin bayan wannan , a hankali RAUDA ta shige jikinsa tana sauke ajiyar zuciya, shima hakan ya saka shi rungumeta sosai yana jin yanzu nutsuwa ke ratsa sasan jikinsa, yanzu yake iya fuskantar rayuwarsa, yanzu ne zai san abinda yake ciki, a yanzu ne zai iya tunani da tunaninsa A hankali ya saka hannunsa yana shafa gadon bayanta har zuwa wajen gashinta dake kwonce a jikinta A nutse ya dan matsar da shi yana sake kallon jikinta dake haukata dukan wani kuzari da nutsuwarsa.......A hankali ya kai lebensa wajen wuyan nata ya ringa ajiye zazafan kisss a duk inda lebensa ya sauka har ya gangaro wajen nata leben dake dantse idannuwanta rintse jikinta na daukan bari bari.....murya cen kurya ya ce" HEY babu wani abin rikicewa fa, saki jikinki mana" A rikicen ta dago idannuwanta da suka rine tana ayana' yau fa ta karewa Rauda' Domin ta riga ta karanci cewar a yau da wahala ta kuma wanyewa da budurcinta, dan irin yadda nasa idannuwan ke fitar da hayaki da gagawa ta so budar bakinta dan ta bashi amsar nan da yake tambayarta wai Abdul danta ne? ko zata samu wani sassaucin? duba da wani tunani da ya shiga ranta, sau dai rana kamanta budar bakin nata ta hadiye maganar sakamakon saukar lebensa a kan nata, lebe mai dauke da dumi da santsin albarka......a dole ta sake lumshe idannuwanta dan karbar sakon nan ko ta wani hali............. A nutse YUSUF ya ringa kokarin sarafata ta hanya mafi sauki da bi a laluma dan baiwa kowani lamari hakinsa har ya kai gabar da ya zama dole ya yi karatun saduwa da iyali bayan ya yi mata a kunnayenta a hankali ya yi mata rumfar da ta saka daga nan ya daina gane komai, domin harta a lokacin da ya dago a birkice dan gannin duniyar nan yau aka fara budeta kuma shine wanda ya fara ratsa ta hakan ya sa ya rukunkumeta dan razanewar da ta yi da bakon lamarin ya bata kyakkyawar rungumar da ya ringa jin kukanta har cikin ransa, sai dai a dole zai kai karshen tafiyar dan ya riga ya yiwa duniyar shigar da ba zai ja baya ba a yanzu dan idan ya ja din wahalar sai ta fi ta farko yawa ...........Ta sha radadin azabar da duk wata kamilaliya cikakkiyar budurwa ke sha a daren ta na farko.........., bale ta hadu da Malamin abin, sai ya zamo ya zama nama daya jal a saman tuwo , ya ririta karshe ya cinye sumul dan ko a yanzu da ya kuma maidata ruwa a karro na biyu suka dawo saman shinfidar da ya cenza da kansa suka sake kwontawa a saman kirjinsa ya dorata idannuwansa a lumshe, jikinsa gaba daya na sake sakewa da lamarinta, babar godiya tana karra tabata ga Ubangijin talikai, wanda bai haifa ba, ba'a haife shi ba, mai rayawa a cikin matace mai kuma kyauta da karri, a rikon nan da ya yiwa RAUDA a saman kirjinsa a irin wannan lokacin , ya sani ne mai kwatarta ko yi masa wasa da lamarinta wanda ya bashi ita ne, ya sani cewa Allah ya dubi lamarinsa ya bashi ba dan halinsa ko isarsa ba, shi yasa zai rike, zai rike da dukkan karfin da Allah ya bashi da kuma adu'a, zai riketa ta hanyar yin takatsantsan, zai bata dukkan kular da ta dace da ita......, in sha Allah zai zamo amini , dan uwa, yaya, aboki kuma miji a duniyarta, zai goga da duk wanda ya nemi lalata farin cikinta, zai girmama wanda ya girmamata! Hucin numfashinta mai dumi dake sauka a jikinsa yake ji har ransa, a hankali bayan ya sake shafa gashin kanta ya budi baki dan karra jaddada mata kalmar da ya fada ya fi a irga a yau, a tausashe cikin nutsuwa ya furta" I love You so much baby........" (☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️😏😏😏😏😏😏😏😏😏😏☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️☹️🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗😌😌😌😌😌😁😁😁😁😁😁😁😍😍😍😍😍😍😍😍😍) 67 Azl PAJIN KARSHE *Tallah, tallah.....tallah manyan hajiyoyina* Bismillahi rahamanin rahim Metaforce online business ne na crypto Wanda aka tabbatar da halaccin sa ,sannan aka tabbatar da cewa ba irin wannan platform din bane da ake gudu da kudin mutane.....domin Metaforce zaka shiga ne da kadan ka dauki da yawa, da wannan Hajia Ummu Khalil wace ke zaune a kasar Nigeria sananiya ce fitaciya ce mai dauke da numbobin waya kamar wanann 07038708382 ta kawo mana hanya mafi sauki dan samun ci gaba.......ku saurara dai *METAFORCE* Yana da level 1_12 Idan Zaki level 1 Zaki Fara da Doller 5,,level 2 Doller 10 ,level 3 Doller 20 Haka dai har 12 YADDA AKE SAMUN ALKAIRI A METAFORCE 💃🏼 Kina Gama register za'a Baki TR coins na adadin level din da kikayi,ko a iya su kin Mai da kudinki fa idan akayi lunching🏃🏻‍♀️🕺😁 .....WASHE BAKI SOSAI HAJIATA....YEAH KO A IYA SHI KIN MAIDA KUDINKI BALE GA WANI DANDANO MAI ZAKI..... *Refferel bonus duk mutum 1 fa idan Kika kawo za'a Baki adadin abinda yasa yayi level din, banda 2 na farkon level 1 da 2* 💃🏼 Ga Kuma garabasa na spillover Ko kin kawo mutane ko Baki kawo ba kina iya samu 💃🏼💃🏼musamman tunda Ni da Zan Miki register Ina aiki sosai (wauh fantastique) Spillover shine zakiga ansa Miki mutum a kasanki ,Kuma a biyaki fa ko Kuma a cike Miki biyu ko dayan farkon nan💃🏼 (magnifique) Da Dollars suke biya idan kinaso Zaki iya siyarwa duk dollers din Kika samu a take a tura Miki kudinki cikin account 💃🏼💃🏼💃🏼 (da wa kika ja Madame?) Metaforce Babu FADUWA Babu asara a ciki...... Ku zo mu kafta duniyar sananu mu samu yanci, nema sai da nema, ki shigo Mu je, kasuwanci mu babu algus ba cuta, zaki kwashi kudinki koda baki kawo kowa ba😍😍😍 sai kun zo tallah2 *MAGANIN KARA KIBA 3IN1* *Ina meneman kiba ido rufe Kuma tanason maganine ingantacce Wanda baida illah kokadan to tazo gadama tasamu yar uwa indai kibace da gyaran nono dakara hips toga Mganinmu nan 3in1 cikin kwana 7 kacal👌🏻 zakiga yadda Zaki fara murmurewa insha Allah mungwada mungani munbayar angwada munsayar angode insha Allah kawata Zaki godemin da 3500 dinki kinhuta da gorin rashin kiba munan cikin Gombe Kuma munatura kaya ko ina kedai tuntumebi ta Whatsapp ko kikirani Kai tsaye ta 08030861857 sai kunzo🥰* *MAGANIN HIPS* *Wannan Maganin anyisane tamasu neman hips sunsha wannan sunsha wannan to gatamunan insha Allah guarantee nakebaki hajiya inada yakini akanta matsala indai tarashin hips ne to anwuce gun 3500 kacal kinhuta kijuya kiwarwasa kisaka kayan gayu kijuyawa Oga yayikallo kawata har yanga saikinmasa ninafadamiki wannan nemeni kisamu naki 08030861857* *MAGANIN NONO* *Itama akwaita me inganci kamarta 3in1 data hips wasu suna korafi nifa nono kawai nakeso yaciko yayi bulbul gwanin sha'awa yadda Oga zaiyaba nasa breast cup suzauna das Amman abun yacitura Nasha Nasha magungunan Amman haryau ba chanji to ganamu Nan yakine ne Dani akansa ba Dan kadanba alhamdullahi duk Wanda yasaya saidai godiyace tsakaninmu kema zokigwada Kuma kigodemin location Gombe 08030861857* Tabas ta wayi gari cikin cenza dukan tunaninta da duk wani yinkurinta na tada bali wa aminanta Atu da saleema , a lokacin da ta wayi gari a cikin jikin mijinta abin kaunarta bayan ya sake jaddada mata abinda ya gana mata tsakiyar dare ya kuma bita da zazafar kula sai ta sake jin cewar lalle zata iya jurewa duk wani motsinsa koda kuwa hakan na neman fin karfinta, zata jajirce ta koyi karatunsa dan zamtowa wajen da zai ringa kawo duk wani motsinsa da bukatarsa ya ajiye, A wannan ranar shi da kansa sai da ya fito daga masalacin sallar la'asar ya leka bangaren Hajia saboda ta bar masa sako a waya cewar Mama zata tafi da Dayana dan kaita asibitin kamar yadda aka bata shawara, kuma tana rokon alfarmar ya mata hanyar samun takardar zaman garin itama dan idan Dayanar ta samu sauki zata so su zauna su jima a cen ta yadda zasu sake samun lokacin karra kusanta kansu da ubagngijinsu, shi yasa ya je da kansa ya kuma basu lokacinsa dan a yau din sun fado a kan daidai, ya kuma da lamarinsu sosai har sai da kunya ta saka maman zubar da hawaye da gaza kallonsa, Allah dai ya nuna mata YUSUF sarkinta ne, kuma dole zata yi masa biyayya ko bata so, ko dan yadda yake kyautata mata ya gama mayar mata da aniyarta a dole suka dawo ita da shi sai gaisuwa kai a kasa dan kunya Mah kuwa dama tunda ya je gaisheta da asubahi ta gane yarensa a dunkule, hakan ya sa ta dauki nauyin girkinsu aka girka aka kawo da ta kula ba zai bar RAUDAR ta zo wajenta ba a yau din sai ta basu lafiya ya kula da matarsa A hankali jikinta ya samu sauki, sabon su kuwa sai da ya zama tamkar zai hanna shi fita fada, abinda ya shafi wayarsa ajiyewa ya yi Taj ne ke kula da shige da ficen abinda ya shafi kasuwancinsa , fada kuwa Bah ne da kansa ke kula da shike da ficen komai, domin kowa uzuri ya masa ya bashi lokacinsa Sannu a hankali ta idasa kwace duk wani gurbi da ya yi saura a tsakaninsu, ya zamo shine ita itace shi, sannan ta dauki duk wani girma da aiyukan da ya dace ace ita ke gudanarwa cikin aminci da kwonciyar hankali, har ya zamo Hajia da kanta ta gama samun sukuni a zuciyarta da tunanin kwarai ko yanzu lokacin ta bar duniya ya zo alhamdulilah Gimbiyar Tsatsunburum gimbiya ce mai adalci, mai riko da addini, mai tausayin talaka Bayan sati Uku da wannan rikicin da kyar Bah ya daina fushi da Mah, suka ci gaba da gudanar da rayuwarsu cikin cencana tsufansu da kare hakkokin junnansu, abokan zamanta kuwa murna ta karra komawa ciki, ya zamo a ci gaba da zaman doya da man jan da suka zabarwa kansu, sai dai na wannan karron ba wani daraja domin wanda suke yi dominsa bai nuna ya san sunna yi ba, sarakuwarsu ta yi watsi da su , kuma sun ci gaba da ci a hannun d'an wace suke yiwa kallon makiyiya, domin basu da yadda zasu yi da zakaran da Allah ya nufa da cara, sun riga sun gane ko ana ruwan mazuru sai ya yi, shi yasa suka koma bakin cikinsu na nukurkusarsu a hankali yana lalata lafiyar jikinsu tsakaninsa da ISHAK sun yi zama mai anfani, domin sun zauna Ishak din da kansa ya bayyana masa tarin damuwar da aka saka shi saka shi, ama a ciki daya bai samu nasarar saka shin ba, domin ko harkar biyan mata ba shine ya saka shi ba shi ya wayi gari a ciki tsundum sanadiyyar ziyartar wajajen da basu da anfani, irin club ɗin da suke zuwa a da, sun yi magana irin ta fahimtar junna sun ci gaba da zumunci da harkar kasuwanci, ama wani ikon Allah kwata kwata baya son Ishak a lamarin da ya shafi RAUDA, sam baima taba bashi damar yin maganar RAUDA ba sai dai su yi na abinda ya shafe su iya su NAJEEBA ta kawo ziyara da yin Barka da tarewa, sun kulla zumunci irin wanda ya dace tsakaninta da RAUDA, ta ji haushin rashin samun wace ta so lakadawa na jaki, haka ta juya Damagaran da jama'arta Tsakanin Mah da Rauda soyaya ce ta uwa da y'a, da farko bayan RAUDA ta fara fita ta so saka matsananciyar Kunya tsakaninta da Mah, sai dai Mah ta ki amincewa da haka, ta ture mata wannan tunanin ta nuna mata ita uwa take a wajenta sarakuwarta Hajia ce ba dai ita ba, dan haka karma ta fara, a ranar ne kuma suka yi shawarar maida auren uncle dinta da tsohuwar matarsa mahaifiyar Abdul idan ya dawo, Mah ta yi amana da haka da farin cikin hakan da kuma adu'ar Allah ya idasa masu nufinsu ___________________________________ Gashin pizza take yi a ovun , dan yau gaba daya da ita ta wuni a ranta, ji take yi idan bata samu ba komai na iya faruwa, shi yasa bayan ta kula ya yi barci ta samu a hankali ta sadado kicin din ta shiga aikin pizzar daga ita sai yar yololuwar rigar barci da Safar hannu dan aiki da ovun din da take yi, hankalinta gaba daya a kan gashin, gani take yi gashin ya fi jimawa fiye da hadin kayan pizzar Har ga Allah bai san ta fita ba, sai da wayar tasu ta tsakiyar dare ta tashe shi shi da Shaheed ya ga ba matarsa, hakan ya sa ya mike ya nufi bayi dan baya jin motsin ruwa da tunanin ko na tsakiyar dare ya kama y'ar gidan Mah ne? dan kawai ya tsokaneta domin har yanzu boyen abin nan take masa abinta, wato sindirki uban dawa mai dawa mai rikita kanshin waje ya koma kanshinsa oga baba mai saka tsoho gudu😌 A lokacin da ya leka ya ga bata nan ne ya ji kamar hankalinsa zai tashi, a hankali ya ce" Shaheed matata bata nan" Shaheed dake masa firar abin haushin da matansa suke son guma masa ya ce" Karta yi nan din mana, aikin banza ai gwarama ace bata nan din, ina maka maganar wulakancin nan na tabata NAJEEBA ta san da maganar yarinyar nan, wai ace ni Shaheed nine suka yiwa kashedin kar su kar su gani ance zuwan yarinyar nan nawa ne? sun manta waye ni? Nine Sarkin damagaram fa, Nine nan mai wukar yanka , kuma mata hudu aka halatta min aura ba biyu ba ko?" Shaheed na fadansa shi kuwa yana leka duk inda ya san zai ganta, ama bai ganta ba, dan bai taɓa kawowa ransa cewar da tsakiyar daren nan y'ar Mah zata je kicin ba, muryarsa a raunane ya ce" Shaheed Allah bata nan, wayo Allahna kirjina ya fara daukan zafi, kai ina matata kar dai aje an shigo an dauken mata" tunanin wannan ya saka shi yin hanyar fita da mugun sauri, gaba daya bai dubi hanyar da zata kai kicin din Bama bale ya gane wani abin Budewa ya yi da sauri bayan ya saka cod ya fito, gaba daya masu bada tsaron nan masu kwana yau suka yiwo kansa , Taj ne gaba gaba suka yi gaggawar zubar da gwuiwowinsu muryoyinsu a tare sunna furta" MALEEK" Taj ya yi gaggawar fadin" Allah ya ja da rai...." suka amshe da " MALEEK " "Allah ya taimaki uban mai uba, marar ubanma ga ubansa nan!" Taj ya sake fada da karfin murya, Tasu muryoyin suka amshe wajen sake furta" MMALEEK" Hannu ya daga masu yana duban Taj kasa kasa ya ce" Kai dilla, ina matata" Taj ya dago ya sake duban idannuwansa da wayar dake hannunsa da alamun bai gane tambayar ba ya dan yiwa girarakinsa alamun karin haske sannan ya furta" Na'am?" Yusuf ya sakar masa harara ya juya dan ya ga sunna son tara masa mutane a nan shi kuwa wa bilahilazi ya zube masu baya ce masa komai a kan RAUDA da sauri Taj ya bi bayansa zai sake tambayar bai gane bane suka jiyo motsi a kicin din cen ciki da alamun aiki ake yi a cikin ido ya dan kura ya nufi hanyar, da sauri Taj ya ce" Allah ya taimakeka, ka bari in fara zuwa, karfe biyu da rabi fa yanzu, kuma bamu da beran daji a gidan nan, motsin kuwa ya yi yawa" Da sauri YUSUF ya riko rigarsa ta sojawa dake jikinsa kiiiii ya juyo shi baya yana sake sakar masa harara ya ce" Kai dila, ka dakata daga cen in beran ne zan yi ihu sai ka shigo, idan matata ce a ciki fa?" Ya karasa fada yana yin cikin, wayar nan a kunne bai kashe kiran na Shaheed ba, shi kuwa ya zauna yana sake zarro ido yana sauraron YUSUF din A nutse ya karasa ya bude kofar kicin din, daidai RAUDA ta duka sosai tana son ciro prmpan din "ALLAHU AKHBAR !" YUSUF ya fada da karfi Shaheed daga cikin wayar ya furta" Beran ne!" Taj ya taho da sauri yana fadin" Subahanallah beran ne, sir dan kauce yau ko Ni Ko shi, manya ne berayen nan na jeji tabas abinci suka biyo!" Juyowa ya yi da sauri ya tare shi yana tura shi baya yace" Kai fita, wai ban hanna kato shigo min nan ba? haba jama'a beran uban wanene Ni, Baby ce!" Da sauri Taj ya fice, Shaheed kuwa ya ringa hailala yana karrawa da kansa ya kashe kiran ya talabe kuncinsa yana tunanin shi kam a aminansa na kusa shi kadai ne mai jin tsoron Allah Saman abin kicin din ya ajiye wayar yana dubanta kamar yadda take dubansa bayan ta ciro din kuma tun da guminsa da komai ta ringa saka abun yankawa tana yankowa a hankali ta kai wajen bakinta bayan ya karaso ta yi bismillah ta cira har tana lumshe ido kasa kasa ta ce" Babyn bae, yinwar ne kaima?" YUSUF ya karaso yana kallon yadda take ci kamar bata ci komai ba, ya yi murmushi yana jin wani boyayan farin ciki a cen kasan zuciyarsa da firar da suka yi da Hajia dazu da safe, tana cewa ya kula da lamarin RAUDA ya bi ta a hankali domin ga dukkan alamu ba ita kadai bace akoy ajiya a tare da ita, kwarai maganar nan ta saka shi farin ciki kuma ya ci gaba da adu'ar Allah ya sa haka din ne, wannan yannayin da ya ganta a ciki ya saka shi jin tabas asibitin fada zai shigo gobe a dubata "Bae, na tsorata fa, da na ga bakya nan, yinwa ce ta tasar min ke? me ya hanna ki kirawo chef ta dafa maki?" Kai ta girgiza ta kawo bakinsa ta ce" Tst it , Tst, ka ji dadinsa kuwa?, wata irin yinwa ce ta hanna min kwonciya shi yasa na fito, kai baka jin ta?" kai ya girgiza ya zauna yana dorata saman cinyarsa a hankali ya ce" Bana ji gaskiya, ama yanzu ina ji" sake kawo masa bakinsa ta yi, ya kuma girgiza kai kasa kasa ya ce " Ba shi ba fa" Tura abinta ta yi a bakinta ta cinye ta hadiye tana jin kwadayin na fada mata a nutse ta ce" To bari in dafa wani abin, me zaka ci?" Idannuwansa da suka gama kadewa ya dora Mata cen cikin makoshi ya furta" ke..........hhhhhhhh" ido ta rintse cike da jin kunya , shi kuwa ya saki murmushi ya mike da ita a jikinsa ya nufi Part dinta dan shi ya fi kusa idannuwansa na sake rufewa............. Alhamdulilah 🤗😍😍😍😍😍😍 Alhamdulilah Nd💓 nd nd nd Mu hadu a sabon littafinmu mai taken *WATA TAFIYAR* Wanda mukai haɗaka Ni da kwatena, wato samira Haruna marubuciyar Badakala, A wata tafiyar tabas akoy wata tafiyar mai ban mamaki, rikici, hargitsi, rikitaciyar soyaya, da sauransu..............................................ku tuntubemu a kan numba kamar haka 93811618 sai mun hade😍😍😍😍😍😍😍😍😍