(Labari mai taɓa zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ *Gabatarwa:-* Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah maɗaukakin sarki. Tsira da aminci su ƙara tabbata ga shugaban halitta, Annabi Muhammad (SAW) tare da AlayenSa. Kamar yanda na fara wannan littafin da IzininSa, ina fatan kammalashi da amincewarSa (Allah maɗaukakin sarki) *GARGAƊI:-* Wannan labarin ƙirƙirrarre ne ba da gaske ba ne. Dan haka ban yarda wani ko wata su juya min labari ta ko wace siga ba. Duk wanda ya cire sunana ko ya ƙara wani abu ba da izinina ba *ALLAH YA ISA BAN YAFE BA.* Dan haka a kiyaye. *GODIYA:-* Bayan na miƙa godiya ga Allah maɗaukakin sarki, dole na miƙa godiyata ga ƙungiyar *NAGARTA WRITERS* saboda sun cancanci yabo da godiya. Allah Ya saka masu da alkhairi a kan namijin ƙoƙarinsu. *JINJINA:-* Dole na miƙa saƙon jinjina ga ƙawayen albarka *RAZ (Rabiatu sk msh and Zarah bb)* Allah ya bar zumunci ya ƙara mana haɗin kai. *SAƘON GAISUWA:-* Ina gaishe da masoyana maza da mata, wanda na sani da wanda ban sani ba. Ku sani cewa Amrah mai ƙaunar duk wani masoyanta ne wanda ta sani da wanda bata sani ba. Fatana a kullum shi ne Allah Ya ƙara mana son junanmu. *ALBISHIRINKU:-* Ina mai maku albishir da cewa gani tafe da wannnan littafi mai ƙunshe da soyayya da ban tausayi, kamar yanda masoyana suke yawan cewa bana masu littafin soyayya to yau gashi nan ina fatan zaku faɗakartu kuma zaku amfana da duk abin da zaku karanta a ciki. 0⃣1⃣ _Ranar talata, karfe 4:25 na yamma._ Sanye take cikin zureriyar hijabi ruwan ƙasa mai hannu. Hannunta wanda ta fiddo wajen hijabin riƙe yake da wata makimanciyar jaka, a ɗayan hannun kuma wayarta ce ƙirar Samsung S7 edge. A hankali cike da natsuwa take taku har ta isa bakin gate ɗin Islamiyar tasu. Ɗalibai ne ke shiga manya da yara, maza da mata. Ɗaga kanta ta yi a dai-dai saman gate ɗin ta kalli rubutun da aka yi wanda fenti ne fari sai rubutun kalar tsanwa an rubuta *MADRASATUL-AMRAH BNT ABDALLAH.* Da larabci aka yi rubutun sai kuma daga ƙasa aka rubuta da hausa. Sunkuyar da kanta ta yi ƙasa bayan ta gama karantawa ta gyaɗa kai hawaye na zirara daga idanuwanta. Cikin makarantar ta nufa kai tsaye ta nufi ajinsu mai suna *FASLUL-KHAMIS (ALIYU BN ABI ƊALIB)* Jiki a mace ta zauna kujerar gaba wadda ita ce kujerarsu. Saurin goge hawayenta ta yi jin Jidda na faɗin "To uwar hawaye. Wani abun ne hala?" Murmushi ta ƙirƙiro tare da faɗin "Babu komai Jidda. Me kika gani?" "Fuskarki na gani kamar kin yi kuka. Kuma na san baya miki wahala dama." Jidda ta faɗa bayan ta dawo bisa kujerar ita ma ta zauna. "Ko kaɗan ban yi kuka ba. Iskan nan da ake ne ina hanya ƙura da ƙasa suka buɗaɗe ni har cikin ido. Shi yasa idona ya canza launi, kuma ga raɗaɗi da yake yi min." "Allah sarki! Ba laifi kam ana iska. Allah Ya kyauta. Yau kin makara, lafiya dai ko?" Ajiyar zuciya ta sauke ta ce "Na yi lecture ne 2-4, ina dawowa a makare ko abinci ban tsaya na ci ba na taho Kuma gashi ma ashe malam bai shigo ba." Kafin Jidda ta bata amsa sai ga wani malami ya shigo hannunshi riƙe da Umdatul-ahkam. Bayan ya yi sallama sun amsa ne suka gaishe shi tare da fito da littattafansu suka buɗo dai-dai inda zasu tashi. Ɗaya bayan ɗaya sai da kowa ta karanto inda aka masu baya sannan malamin mai suna Malam Yusuf ya yi masu ƙari kasantuwar ya ga mafi rinjaye sun fahimci darasin da ya gabata. Yana fita Mallam mai Fiqhu ya shigo shima ya masu darasin sannan aka tashi daga makarantar. Bayan sun fita sai da budurwar ta sake ɗaga dara daran idanuwanta ta kalli sunan Islamiyyar cike da tausayi sannan ta sunkuyar da kanta ƙasa ta tafi gida. A zuciyarta tana mai tsananin ƙagara ranar jumu'a ta yi. *** Da sallamarta ta shiga gidansu wanda yake ba wani babba sosai ba, sai dai daka ga gidan ka san suna da rufin asirinsu bakin gwargwado. Wata matashiyar mata wadda ba zata wuce shekara talatin da biyar (35) ba ta amsa sallamar tana murmushi ta ce "Maryama an dawo?" "Na dawo Mama. Aiki ake?" Ta tambaye ta bayan ta ƙarisa shiga Kitchen ɗin. "Wallahi kuwa. Abbanki ne ya kirani wai yana son tuwon dare, shi ne fa na tashi da azama na ɗora masa. Har ma na gama tuwon miya ce ta rage." Maman tata ta faɗa tana zuba man-ja a tukunya. "Kawo na ƙarisa miki Mama." Maryama ta cire hijabinta ta rataye a kan ƙofar kitchen ɗin haɗe da jingine jakarta jikin bangon kitchen. "A'a Maryama. Ke da kika dawo daga makaranta? Na tabbata a gajiye kike, saboda ko abincin rana baki ci ba kina dawowa daga lecture kika yi shirin islamiya. Je ki cire Uniform ki zo kafin nan na zuba miki abinci." "Wallahi Mama bana jin yunwa. Ki kawo na miki tun da dai ba wani aiki nake ba. Kullum ina makaranta ke ce kike yin komai. Dan Allah ki bari ni ma yau na samu wannan ladar." Mama ta murmusa ta ce "Tun da dai kin matsa gashi nan ki ƙarisa. Allah Ya miki albarka ke ma Ya haɗa ki da wanda zasu kyautata miki kamar yanda kike kyautata min." "Amin Mama." Ta faɗa haɗe da karɓar ludayin miyar ta kwashe jajjagen tarugu da albasa da daddawa dake cikin turmi. Cike da natsuwa Maryama ta kammala miyar busasshiyar kuɓewa ta barta a buɗe dan kar ta rufe ta tsinke. Hijabi da jikarta ta ɗauka sannan ta nufi ɗakinta domin gabatar da sallar magrib. Bayan ta gama ta zauna ta yi adhkar har lokacin isha'i ya yi sannan ta fito sanye da dogon hijabi har kasa ta nufi ɗakin Abbanta. Zaune yake shi da Mamanta sai kuma ƙaninta zaune a kasa. Cikin ladabi ta gaishe da Abban nata sannan ta ce "Sannu da hutawa Mama." Ta zauna a ƙasa kusa da Muhammad. "Yauwa Maryama. Ai ke ke da sannu." Ta mata murmushi. "Yaya Maryama sannu da aiki." Muhammad ɗan kimanin shekara goma sha biyu ya faɗa. "Yauwa ɗan albarka. Ya tahfiz ɗin?" Ta tambayeshi. "Akwai wahala Yaya. Ko yau na sha zana duba bayana ki gani." Ya faɗa yana ƙoƙarin ɗaga rigarshi ta baya. "Ba sai ka ɗaga min ba dan ba tausayinka zan ji ba. Ban san me ya sa ba Muhammad baka son karatu." Ta faɗa bayan ta haɗe fuskarta babu alamun wasa. Cikin sigar a tausaya masa ya ce "Ina fa karatu Yaya. Malamin namu ne..." Ta yi saurin dakatar da shi, "Kar ka ma malaminku sharri. Idan baka masa laifi ba ai ba zai dake ka ba. Ka ringa karatu sosai kuma ka guji aikata laifi ka ga idan akwai malamin da zai taɓa lafiyarka." Shiru ya yi kafin ya yi dariya abinku ga ƙaramin yaro ya ce "Kuma fa Yaya kin yi gaskiya. Kin ga Haneef shugaban ajinmu ba'a dukansa saboda kullum sai ya bayar da harda babu tangarɗa. Kuma baya laifi ko kaɗan." "Ka gani ba. Kai ma sai ka yi koyi da shi ai, idan baka son duka." Ta faɗa tana masa murmushi. "To Yaya. Bacci nake ji ma." Ya yi hamma. "Bara na kawo mana tuwo sannan kaci ka yi bacci ko?" Ta miƙe tsaye. Mama ta ce "Ai ni dai kawaici na yi dan na ga kuna fira da Muhammad. Yunwa nake ji wallahi." Abba ya ce "To ai gashi nan zata kawo yanzu" Ya murmusa. Ta nufi kitchen tana murmushi. Misalin karfe tara suka kwanta kamar yanda suka saba da wuri suke kwanciya bacci gidan. *RANAR JUMU'AH 10th January 2015* Ranar da Maryama ke tsumaye ke nan. Ranar data matsu ta yi har tana ganin tsayin wannan ranar. Pinky durling💗 RAZ 2 [8/30, 3:27 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 0⃣2⃣ A k'agare take ta iso gida domin tafiya Islamiya, amma wani Malaminsu ya rik'e su har kusan k'arfe biyar na yamma. Yi take tana duba agogon wayarta, baki d'aya hankalinta ya koma ga ta tafi, har wasu hawaye take ji suna k'ok'arin fito mata. Jin hak'urinta ya k'ure ya sa ta tattara ya-nata ya-nata ta mik'e tsaye, tun kafin ta fito daga row d'insu ta ji muryar malamin yana masu bankwana alamun ya gama lecture d'in ke nan. Ajiyar zuciya ta sauke, had'e da godiya ga Allah sannan a hanzarce ta fita, ko k'awar tata ma bata tsaya jira ba. Course mate d'insu Saifullahi ta gani bisa mashin d'inshi da alama yana jiran wani ne, amma Maryama sai da ta rok'e shi a kan ya taimaka ya tafi da ita sauri take. Bai ko musa mata ba ya ce ta hau su tafi. A maimakon ta kwatanta masa gidansu sai bata yi ba, islamiyyarsu kai tsaye ta sa ya kaita. Cikin mamaki Saifullahi ya ce "Yau Friday ana Islamiyya ne Maryam?" "Ba darasi zamu yi ba Saif, akwai abin da muke ne." Ta bashi amsa tana mai k'ok'arin sauka daga bisa mashin d'in. "Na gode k'warai Allah ya bar zumunci." "Ameen Maryama. Allah ya bada sa'a. Sai anjima." Ya tada mashin d'in ya tafi. A gaggauce ta isa bakin gate d'in, ta samu mai gadin zaune da radio rik'e a hannunsa. "Sannu Baba. Mun yi da kai da an yi la'asar zan zo kuma sai gashi na kasa cika al-k'awari ko? Yi hak'uri, wallahi wani malaminmu na tsaya ya sallame mu." Murmushi dattijon yayi ya ce "Babu komai ai. Kina lafiya ko?" "Lafiya lau Baba. Mu tafi gidan nasu ko?" Ta tambaye shi. D'aga mata kai ya yi tare da jawo 'yar k'aramar k'ofar da ke jikin gate ya rufe da kwad'o sannan ya soka makullin a al-jihunsa. Mashin d'insa ya hau sannan ita ma ta hau daga baya suka kama hanyar unguwar Gidan dawa da ke cikin Birnin Katsina. Tafiya mai nisa ce ta sada su da gidan, kasantuwar akwai 'yar tazara daga Islamiyyar. Bayan sun isa Malam Sallau ya kashe babur d'insa sannan ya ce "To Maryama mun iso, kin ga gidan nan." K'ok'arin sauka ta yi a hankali bisa rashin sani har k'afarta ta d'an gogu a salansar mashin d'in, ta k'one kad'an. "Subhanallahi!" Ta furta a hankali bayan ta k'arisa saukowa. "Bi a hankali dai Maryama." Ya fad'a bayan ya gyara tsayuwar babur d'in. "Mu shiga ko?" Ta fad'a cikin sanyin murya. "Anya kuwa? Ki shiga dai, ki sanar da su idan sun bani izinin shiga sai in shigo." Kallonshi ta yi kamar kar ta yi magana kuma dai ta daure ta ce "To Baba ai kuma basu san ni ba." Da murmushi ya ce "Babu komai ai. Ki shaida masu cewa tare kike da Mallam Sallau, ba damuwa." D'aga kai ta yi tare da shiga cikin gidan da sallama k'unshe a bakinta. Gida ne ginin har k'asa irin na da, wanda kallo d'aya zaka masa ka tabbatar cewa gidan mabuk'ata ne. Shiru ba'a amsa ba hakan ya bata damar sake yin wata sallamar nan ma dai shiru. Sai a karo na uku sannan ta ji muryar dattijuwa ta amsa sallamar tana k'ok'arin fitowa daga cikin d'aki. Ganin Maryama ya sa ta d'an saki murmushi irin ba wai dan ta santa ba, sai dan karamci kawai. "Barka da zuwa. Iso daga ciki mana." Matar ta fad'a fara'a k'unshe a fuskarta. Kai ta d'aga alamar to, sannan ta k'arisa ciki. Tabarma matar ta shimfid'a mata sannan ta bata izinin zama ta zauna. "Sannu Mama. Ina yini." Maryama ta furta cikin girmamawa. "Lafiya k'alau 'yan mata. Sannu fa." Ta fad'a cikin rashin wayarta. "Tare nake da Mallam Sallau, yana waje." Ta fad'a tana kallon Matar. "Allah sarki! Yo to kuma ai da sai ya shigo ko? Shi dai Mallam Sallau kullum kamar bak'o. Dan Allah je ki k'ira sa da sauri. Mallam!" Ta k'walawa mai gidanta k'ira. Tashi Maryama ta yi ta nufi waje tare da k'iran Mallam Sallau. Tana gaba yana biye da ita suka shigo ciki. Matar ce zaune a bisa tabarmar sai mai gidanta a kusa da ita yana murmushi. Mik'ewa ta yi da sauri ta ce "Mallam Sallau zauna daga nan. 'Yan mata zo mu shiga daga ciki ko?" Da sauri Mallam Sallau ya ce "Ahh babu damuwa, ku zauna kawai, ai magana zamu yi." Hannu ya mik'awa mutumin zaunen suka gaisa sannan ya zauna a kusa da shi. Maryama kuma aka shimfid'a masu wata tabarmar suka zauna tare da matar. Bayan sun gama gaggaisawa ne Mallam Sallau ya ce, "Wannan yarinyar sunanta Maryama. D'aya daga cikin d'aliban Islamiyar *AMRAH BNT ABDALLAH.* Ta jima tana son sanin tarihin rayuwar *Amrah* tun daga lokacin da aka yi wani wa'azi; wanda Malamin ya d"auko zancen *Amrah* tun bai yi nisa ba kuma sai lokaci ya k'are. Tun daga lokacin take son sanin *Wacece Amrah?* ta same ni da maganar ya fi sau biyar, tun ina gudunta da maganar dai har na ce ranar wannan jumu'ar ta zo zan kawo ta domin ta ji daga gare ku. Ina fatan hakan ba zai zama takura ba." Kallonsu suka mayar ga Maryama da ta d'an sunkiyar da kanta k'asa tana wasa da 'yan yatsun hannunta. Matar ta ce "Allah Sarki!" Tare da share d'an siririn hawayen da ya fito mata. Shi kuwa mutumin cikin k'arfin hali ya ce "Babu wata takura Mallam Sallau. Sai dai kuma gashi yamma ta yi yanzu magrib ta gabato." Mallam Sallau zai yi magana Maryama ta yi saurin fad'in, "Ehh wallahi. Babu damuwa ai ko gobe ma sai in zo ko da ni kad'ai ce. Tun da dai mun zo tare na ga gidan." "Haka ne. Allah Ya kaimu to." Mutumin ya fad'a. Cikin k'arfin hali Matar ta ce "Insha Allahu gobe zaki ji tarihin rayuwar *Amrah.* Zaki san ko wacece *Amrah Bnt Abdallah.* Ta sake share hawayen bisa kumatunta. Sosai Maryama ke mamaki, lallai ta yarda cewa babu abin da ke cikin *Rayuwar Amrah* face tsabar tausayi, duk da yake bata san komai ba, abin da ta sani dai kawai ita Amrah d'in mace ce mai matuk'ar halin kirki, wacce ke da tarihi mai kyau kuma abin koyi. Bankwana suka yi ta masu godiya sosai sannan suka fita waje ita da Mallam Sallau. Har gida ya kai ta ta masa godiya sosai ta shiga ciki. Tana shiga bata samu kowa a tsakar gida ba, kai tsaye ta zarce ciki. Muhammad ne da gudu ya rungume ta yana fad'in "Yaya Maryama kin dad'e fa. Ina ta jiranki ki dawo ki koyan karatu, gashi gobe da sassafe zan bada harda kuma ban iya ba." Da murmushi ta ce masa "Wallahi Muhammad na je wani wuri ne bayan na tashi daga makaranta. Amma gashi na dawo ai yanzu sai mu yi. Mama fa?" "Tana cikin d'aki yanzu Baba ya dawo ne. Zaki koyan yanzu ko sai an yi sallah?" Ya tambaye ta. "Bari a yi sallah tukuna. Ka ga fa ko abinci ban ci ba. Kar ka damu insha Allahu zan koya maka har sai ka iya sannan zamu daina." Ta sakar masa murmushi. Shi ma murmushin ya sakar mata ya ce "Allah Ya yarda Yayata. Ki je yanzu ki yi wanka ki ci abinci ko?" Kai ta d'aga masa sannan ta shige d'akinta. Jakarta kawai ta ajje sannan ta yi wanka ta fito Ta samu har Mama ta kawo mata abinci ta rufe da plate, ga kuma abin sha nan a jug da k'aramin cup Murmushi ta yi mai cike da nuna jin-dad'i, "Wayyo Mamana. Allah Ya saka miki da alkhairi." Ta fad'a sannan ta zauna ta fara ci. Zuciyarta cike da tsumayen gobe ta yi, duk da yake cewa akwai Islamiyya kuma bata son ta yi fashi amma fa bata jin zata iya hak'ura har a tashi. Ta k'udurta cewa da yardar Allah gobe k'arfe goma a gidan su Amrah zata mata. Bayan ta gama ne ta koyar da Muhammad karatu har ya iya sosai sannan ta koma d'akinta. Wayarta ta latso lambar Jiddah, babu jimawa kuwa ta d'auka. Sallama ta yi bayan sun gaisa ne take shaida mata cewa idan ta je Islamiyya gobe ta fad'a ba zata samu damar zuwa ba, akwai inda take son zuwa ne. Jidda ta ce "Kin manta gobe akwai rehearzal (Gwajin koyo) k'arfe tara? Da dai kin yi hak'uri Maryama, ko idan kika yi naki ne sai ki tafi." Jinjina kai Maryama ta yi ta ce "Jiddah kin san fa ba lallai Mallam Ahmad ya bar ni tafiya ba duk iya k'wa-k'wata kuwa. Gashi kuma inda zan je yana da matuk'ar muhimmanci." "To shi ke nan babu damuwa. Zan sanar ma Mallam Yusuf shi ne mai sauk'in kai. Allah Ya taimaka." Murmushi Maryama ta yi ta ce "Yauwa na gode k'warai Jiddah. Sai da safe, ki gaishe da Mami." "Zata ji." Ta tsinke wayar. Jikin chaji ta jona wayar sannan ta koma ta kwanta. A zuciyarta tana nazarin wata magana wadda ita kad'ai ta saka ta fashewa da kuka. Juye-juye kawai take yi bacci ya k'i d'aukarta, da k'yar ta samu ya d'auke ta a lokacin har sha biyun dare ta wuce. Pinky durling💗 *RAZ 2👌🏻* [8/30, 3:28 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 0⃣3⃣ Washe gari tun da safe ta tashi ta hau shiri, k'arfe bakwai da rabi Muhammad ya shigo da gudu yana fad'in, "Yaya Maryama na shirya, wai ki fito in ji Baba." Juyowa ta yi ta kalle shi ba tare da ta ce komai ba, sai dai kuma kallon da ta masa kawai ya isa ya tabbatar masa da laifinsa. "Yi hak'uri Yaya Maryama." Ya fad'a a marairaice. "Oya get out." Ta gwada masa k'ofa da hannu. Kama kunnuwansa ya yi ya ce, "Zan yi yanzu Yaya." Ya fita daga d'akin. "Assalamu alaikum." Ya fad'a da k'arfi wanda har sai da dariya ta nemi k'wace ma Maryama. Amsa sallamar ta yi ta ce "Ko kai fa. Ka tafi kawai Muhammad. Ka ce da Baba akwai inda zan biya ne kafin in tafi. Kar in tsaida ku kuma na san tahfiz d'inku babu wasa. Ka ga ko karyawa ma ban yi ba." "To shi ke nan Yaya. Na tafi." Ya yi gaba. Addu'a ta masa sannan ta ci gaba da shirinta cike da natsuwa, wanda dama halinta ke nan, komai nata a natse ne, slow d'in nata ma har ya yi yawa kamar wacce k'wai ya fashe mawa a ciki. Misalin takwas da kwata ta gama shiri ta fito falo, Mama ta samu zaune da littafin hisnul-muslim a hannunta tana karantawa. Ganin haka ya sa ta nufi kitchen, ruwan lipton ta zubo sannan ta zuba soyayyar doya a plate ta dawo falon. A hankali take karyawa har ta gama sannan ta fitar da kayakin ta kai su kitchen. Ko da ta dawo har Mama ta gama adhkar d'in. Gaishe ta ta yi sannan ta ce, "Mama har an gama?" Da fara'a Mama ta ce, "Wallahi kuwa na gama Maryama. Ya aka yi yau kika makara? Na san halin malaman nan naku fa wani lokaci ba sani ba sabo ne." "Ai da yake yau zamu fara rehearzal ne Mama. Duka d'aliban ma za'a ke fiddowa a fili muna yi a gabansu. Tun daga nan har lokacin walimar." Maryama ta bata amsa tana k'ok'arin zura hijabinta da ta ninke ta d'ora a bisa hannun kujera. "Af! To masha Allahu! Allah Ya taimaka. Dawowa ba yanzu ba ke nan ko?" "Gaskiya kam Mama. Wata k'ila ma ta-zarce zamu yi har shida na yamma sannan mu dawo." Maryama ta fad'a, ba kuma 'karya ta yi ba, haka tsarin abun yake, sai dai kuma ita kam ba can zata nufa ba, sai idan ta gama abin da take da wuri ne zata je ko da da yamma ne. "Bara na tafi Mama." Ta fad'a tana k'ok'arin fiddo hannunta daga hannun hijabin. "Allah Ya bada sa'a. Sai kin dawo." "Ameen Mama." Ta fita daga d'akin. Sai da ta koma d'akinta ta d'auko kud'i sannan ta fita. A dai-daita sahu ta tsayar ta kwatanta masa unguwar. K'arfe tara da minti ishirin ta mata a k'ofar gidan su Amrah. Bayan ta sallami mai adai-daita ta shiga gidan da sallamarta. Amsawa matar gidan ta yi sannan Maryama ta shiga ciki da fara'a. "Sannu da zuwa Maryama. Iso ciki." Ta fad'a cikin karramawa. Shigowar kuwa ta yi har falo matar ta kai ta. Wasu irin tsofaffin kujeru ne irin wanda sun ji duniya d'in nan, katifar jiki duk ta gama lalacewa sai zallar katako wanda idan mutum bai kula ba ma tsaf zai iya jin ciwo. Bayan ta zauna matar ta ce, "Bara na kawo miki koko. Sai dai kuma yanzun nan na ba almajiri k'osan, saboda kar ya sandare kuma ba cinsa zan yi ba, kokon ma a samus na zuba shi ne." "Wallahi Mama ki bar shi na gode. Sai da na karya ma sannan na baro gida." Maryama ta fad'a. "Eyyah! To shi ke nan ai. Ina zuwa." Ta fita daga falon. Babu jimawa sai gata ta dawo, zama ta yi daga d'an nesa da Maryama san nan ta ce, "Yanzu zan baki labarin Amrah, Maryama." Gyara zama Maryama ta yi ta ce, "To ina jin ki Mama." "Sunanta ke nan na yanka Amratu. Amrah muke kiranta da shi ni da mahaifinta. Amrah ita ce 'ya ta uku a gidan nan, sai dai kuma matsayin ita ce babba, kasantuwar duk yaran da muka haifa basa rayuwa. Tun daga lokacin da muka haifi Amrah, mahaifinta ya d'auki soyayyar duniya ya d'ora a kanta, yake bata kulawa sosai fiye da sauran yaran da muke haifawa basa rayuwa. Tun Amrah na da shekara d'aya a duniya take da wani laluri, na yawan k'ai-k'ayin tafin k'afa da kuma tafin hannu. Abin mamamki, yarinyar da bata san wani abu ba a duniya, amma duk lokacin da tafin k'afarta ko hannunta ya dame ta da k'ai-k'ayi, da 'karfi zata kama hannuna ko na mahaifinta tana kai wa a inda yake mata k'ai-'kayin, da nufin a sosa mata. Tun bamu fahimtar komai har ta kai ga mun fara fahimta, wato dai suna damunta da k'ai-'kayi ne. A lokacin da ta cika shekara biyu a duniya ne kuma cututtuka suka fara nata yawa, wato yawan zazzab'i, sannan kuma da yawan ciwon gab'ob'i. Yarinya k'arama 'yar shekara biyu, wacce ko maganar kirki bata iya ba, amma ta san ta ringa gwada duk inda ke mata ciwo tana fad'in, "Hannu ciwo, cici ciwo, kai ciwo..." da dai sauransu. Tun bana d'aukar abun serious har na fara damuwa, saboda har cikin dare idan abun ya tasar mata ko kad'an bama bacci, ita kuka ni kuka, mahaifinta ne kawai mai dakewa, yake k'arfafa min guiwa a ko da yaushe. Ga ta da yawan yin zazzab'i, da zarar sauro ya cije ta sai zazzab'i, idan ta fara zazzab'in kuma shi ne sai wannan ciwon gab'ob'in wanda yake rikita mana lissafi. Duk wannan abin da yake faruwa, ciwo da yake ta addabar Amrah, ko da wasa bamu tab'a gwada kai ta asibiti ba. Wani lokacin idan zazzab'in ya dame ta ne da kanshi Babanta yake zuwa chemist cewa 'yarsa na zazzab'i, sai a bashi maganin zazza'bin kawai ya zo a bata. Wata rana, k'anwata ta zo daga Kaduna, ta zo ganin gida shi ne ta zo min wuni, ta samu Amrah bata da lafiya, na tasa ta a gaba ina mammatsa mata duk gab'ob'inta da take gwada min suna mata ciwo. Cikin tausayi ta ce, "Wai Yaya Murja me yake damun yarinyar nan ne? Abin tausayi har ta iya fad'in inda ke mata ciwo? Alamun ma ta saba ke nan." Gyad'a kai na yi na ce, "Zainabu ni kaina ban san me yake damun Amrah ba. Sai dai kawai na san zazza'bi ne idan ta yi shi yake sakar mata ciwon gab'ob'in nan. Tun da nake haifar yarana suna mutuwa ban tab'a had'uwa da mai irin ciwon da Amrah ke yi ba. Zainabu na fara tsorata sosai wallahi." Ta fashe da kuka tana kallon Amrah. Ita kam Amrah baki ta wangale tana dariya, shi k'aramin yaro dama babu ruwanshi, yanzu zai gama kukan ciwo kuma yanzu zai kama dariya. Zainabu ta numfasa sannan ta ce, "Kuma ku baku tab'a kai ta asibiti ba?" "Bamu tab'a ba Zainabu. Sai dai kawai Babanta da yake siyo mata magani. Yanzu haka tana da sauran panda yana nan bai k'are ba." Na bata amsa. "Gaskiya Yaya Murja ku daure dai ku kai ta asibiti. Kar a je ana ciwo daban, magani daban. Likita bashi da halin bada waraka, sai dai kuma yana bada tashi gudunmawar. Ki daure dai a kai ta d'in." Shiru na yi ina nazari a azuciyata. Na san tabbas gaskiya Zainabu ta fad'a min, sai dai kuma babu hali ne. Abincin da zamu ci ma wahala yake mana. Kuma ba wai zuwan ne nake ji ma ba, a'a, kud'in da za'a caje mu nake ma. Tun da dai komai na yanzu ya koma na kud'i. "Kin yi shiru Yaya Murja. Gaskiya nake fad'a miki fa. Bai kamata ku zauna kuna ji kuna gani ciwo ya ringa cin yarinya ba. A ce wai yarinya da zarar ta yi zazzab'i sai k'asusuwanta su hau ciwo? Gaskiya akwai dai wata matsalar daban, ba wai zallar zazzab'i ba ne." Cikin k'arfin hali na ce, "Insha Allahu ranar litinin zan kai ta asibiti. Ni kaina abin yana damu na bani da yanda zan yi ne." "To Allah Ya kai mu Yaya Murja. Allah kuma Ya bata lafiya." Ta mik'e. Bankwana muka yi sannan ta tafi ta bar ni da tunanin kalamanta, hawaye na zirara daga idanuwana zuwa kumcina. Pinky durling💗 *RAZ 2👌🏻* [8/30, 3:28 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 0⃣4⃣ Sai dare sannan mahaifinta ya dawo, a gajiye lis yake, wanda kallo d'aya zaka masa ka tabbatar da baya tattare da walwala. Duk da cikin halin da nake, na tausayin ciwon Amrah, bai hana ni tashi na tarbe sa ba. "Sannu da dawowa Mallam. Zauna ka huta kafin na kawo maka abinci." Na fad'a ina mai k'ara dubar yanayinsa. "To Murja." Ya fad'a jiki a sab'ule. Kitchen na nufa na zubo masa dafadukar shinkafa da na ajje masa, na d'ibo ruwa daga tulu na kawo masa. Sai da ya ci ya yi nat, na tabbatar ya samu natsuwa sannan na ce, "Allah dai Ya sa an yi nasara." Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya ce, "Babu nasara Murja. Abin dai sai hamdala kawai." Ya kalle ni ya gyad'a kai, sannan ya ci gaba da fad'in, "Duk yinin nan guda da muka sha, wai Alhajin ya fasa zuwa. Har fa lokacin da na ga magrib ta yi na ce ni dai zan tafi, wasu suka ce in dai k'ara ha'kuri, an tabbatar cewa yana gari wai zai zo. 'Yar d'ari biyun da nake da ita, da ita na ci abinci da rana, naira ta hamsin d'aka da waje yanzu haka. Ban san ya zan yi ba Murja. Talauci babbar cuta ce, wacce samun maganinta yake da matuk'ar wahala." Ya dafe kansa. Cike da tausayi na ce, "Sai hak'uri Mallam. Ta ko wace hanya Allah Yana jarrabtar bayinSa. Hakan kuma ba wai yana nunar da baYa sonmu ko kuma Ya manta da mu ba ne, a'a, na tabbatar cewa mun fi wasu, tun da mu da wuya mu rasa abin da zamu ci. Wasu kuwa babu, abin da zasu saka ma cikinsu ma wata wahala ne. Fatana dai kawai Allah Ya bamu ikon cinye wannan jarabawar." "Ameen. Wai duk jiran nan da muka yi, sai bayan isha'in nan wani d'an korensa ya zo yana fad'in mu tafi, wai Alhaji ba zai samu zuwa ba, sai kuma wani lokacin. Dama kyauta ce ya yi niyya ba rok'arsa aka yi ba, kuma wani uzuri ya sha gabansa." "Shi ke nan ai Mallam. Ka cire damuwa daga ranka. Allah Yana tare da mu..." tun ban rufe baki ba Amrah ta fasa kuka tare da tashi zaune, saboda dama tun d'azu ta yi bacci. Da sauri na kama ta na d'ora a bisa cinya, ina rirrigarta a hankali had'e da tofa mata addu'o'i, dan a tunanina ko firgita ta yi ne. Abin mamaki sai d'ago min hannunta ta yi, cikin maganarta da bata gwanance ba ta ce, "Umma hannu ciwo.." ta kuma fashewa da wani kukan. Gyad'a kai na yi cike da tausayi, na kama hannun nata a hankali ina mammatsawa ina tofa mata addu'a har na samu ta yi shiru. Bayan kamar mintuna biyar ta ce, "Umma ya daina ciwon." Ta sakar min murmushi. "To ki gode wa Allah kin ji 'ya ta? Allah Ya baki lafiya da duk kan 'yan uwa musulmai." Na fad'a ni ma ina mata murmushin. Bakinta dama ya dad'e da sabawa da furta amin, hakan ya sa ta ce, "Ameen Umma." Ta sauka daga jikina da sauri ta nufi mahaifinta, saboda sai a lokacin ma ta kula da shi. Saurin kawar da damuwarsa ya yi ya d'auke ta, "Amrah 'yata sannu kin ji? Insha Allahu zaki samu lafiya ke ma kamar kowa." Bata ce komai ba sai lafewa da ta yi a jikinsa, take bacci ya d'auke ta. Tabbatarwar da muka yi ta yi bacci ya sa a hankali ya nufi uwar d'aka da ita, ya kwantar sannan ya nufi yin sallah. Bayan ya gama a lokacin nima na shigo d'akin har ma na kwanta a kusa da Amrah, ya hau gadon zai kwanta na yi saurin mik'ewa na ce, "Ka gaji ko? Da alama kwanciya kake son ka yi. Gashi kuma ina son da mu yi wata magana." Bayan ya hau gadon ya ce, "Babu komai Murja. Ina saurarenki." Saurin share k'wallata na yi sannan na ce, "Dama gani na yi ya kamata mu kai yarinyar nan asibiti, sam bamu kyauta ba zaman da muke yi haka da ita, ba tare da sanin halin da take ciki ba. Mallam ban tab'a jin yaro mai irin lalurin Amrah ba, rayuwata tana matuk'ar dugunzuma a duk lokacin da ciwon yarinyar nan ya taso, tana matuk'ar bani tausayi. Tun bata san miye ciwo ba har ta kai ga ta sani yanzu. Yarinya 'yar shekara biyu da watanni amma har ta san ciwukanta." Cike da tausayi Mallam ya ce, "Haka ne Murja. Ni ma kaina na jima ina wannan tunanin, ina jin tausayinta sosai musamman yanda har cikin dare ba wani baccin kirki take samu ba. Ya kamata mu je asibiti, idan ma wani ciwon ne sai mu sani, mu bi dokokinsa ko ta samu sassauci." Cikin kuka na ce, "Haka ne Mallam." Ajiyar zuciya ya yi sannan ya ce, "Gashi kuma bani da kud'i Murja. Ban ajje ba ban ba wani ajiya ba. Na abin hawa ma kanshi babu bare kuma na sauran hidindimun asibiti. Wayyo ni Abdallah!" Sai ga hawaye suna zarya a bisa kumcinsa. Duk da ni ma ina jin hawayen amma a haka na daure, shi ya koma macen ni kuma na koma namiji, na ci gaba da rarrasarsa har na samu ya yi shiru. "Akwai 'yan samiruna da tasoshi tun na aure, suna wancan d'akin na ajiya tun-tuni. Insha Allahu da sassafe zan je gidan Rakiya Dillaliya, wata k'ila zata siya. Ko nawa ne ma dai ta bamu mu samu a kai ta asibitin. Ai ya fi mu je maula ana wulak'anta mu." "To shi ke nan Murja. Allah Ya kai mu goben Ya sa a yi nasara." Ya furta a hankali. "Ameen Mallam. Ka kwantar da hankalinka, Allah'n da Ya d'aura mata wannan cutar shi zai warkar da ita, insha Allahu zata warke, ta murmure kamar sauran yara." Murmushi ya yi sannan ya ce, "Ina fatan haka Murja. Na gode k'warai Allah Ya miki al-barka." Da murmushi ni ma na ce, "Ameen Mallam." Daga haka bacci ya d'auke mu. *** Washe gari kuwa tun da sassafe na fiddo 'yan tarkacen da zan siyar, sun yi k'ura sosai saboda sun kai kusan shekaru biyar a ajiye cikin d'akin ban fitar ba. Bashin omo na ci na wanke su tas, har shek'i suke yi sannan na kife suka bushe. Buhu na nema mai tsafta na saka a ciki, sannan na nufi gidan Rakiya Dillaliya. Da yake Allah ya duba zuciyarmu, kyakkyawar niyya ce a ciki, babu ko b'ata lokaci Rakiya ta siyi kwanonin, cas ta cake min naira dubu takwas da d'ari biyar. Na matuk'ar jin-d'adi, da murna na nufo gida, zuciyata sayau, tamkar an ce min Amrah ta warke ne. Sai da na fara biyawa na biya ku'din omo, sannan na siyo mana bredi da sauran kayan shayi, sai da dai na kaso dubu d'aya sannan na iso gida. Ko da Mallam ya ga fuskata ya san akwai nasara, ga uwa uba leda a hannuna cike da karikitai. "Mallam ta siya har dubu takwas da d'ari biyar." Na fad'a masa ina dariya. Shi ma dariyar ya yi ya ce, "Ahh lallai abu ya yi kyau. Ta kyauta sosai wallahi." Halawartsinke na fiddo daga cikin ledar na mik'a wa Amrah, da sauri kuwa ta karb'a tana dariyar jin dad'i. Kitchen na je na dafa mana ruwan zafi, na zuzzuba mana sannan na zuba kayan ha'di. K'arfe goma da rabi muka gama, na ma Amrah wanka muka shirya sannan muka fito, Mallam ya rufe gidan muka nufi bakin titi. Bamu jima ba muka samu keke napep, asibiti muka ce ya kai mu, ya tambaya, "Mallam wace asibitin zan kai ku?" Shiru muka yi mu duka dan bamu san inda zamu je ba, hakan ya sa ya sake maimaita mana. "Wace asibiti ce ka sani wacce ake kula da k'ananan yara sosai?" Mallam ya tambayi matashin. Shiru ya yi jim kad'an sannan ya ce, "Ku je asibitin Turai, dama ta yara da masu ciki ce kawai ai." Ya fad'a yana kallon Mallam. "In haka ne, ai ga Turai d'in can ma babu nisa sosai ko? A nawa zaka kai mu?" "Ku kawo d'ari da hamsin." Ya fad'a. Shiga ciki muka yi ya kai mu har cikin asibitin, dama kuwa babu nisa daga gidanmu, duk cikin unguwa d'aya ne sai dai kuma dole mutum ya hau abin hawa, idan ba haka ba kuma akwai gajiya. Bayan mun shiga reception, muka tambaya abin da ya kamata mu yi, wata mata ta ce sai mun sai mata kati kafin komai. Mallam ya je da kanshi ya sai mata katin aka cike, sannan aka d'ora a layin ganin paediatrician (likitan yara.) Har bayan azahar layi bai zo kanmu ba, kusan k"arfe biyu aka kira sunanta. Likita ce mace, sanye da lab court da medical glasses. Kujerar dake fuskantarta ta bani izinin zama, bayan na zauna na gaishe ta da sakin fuska ta amsa. "Me yake damunta ne?" Ta tambaye ni tare da mik'o hannu ta karb'i Amrah. "Dr. Tak'amai-mai ban san me yake damunta ba, saboda wannan ne karo na farko da na kawo ta asibiti. Kawai dai na san ta jima tana fama da k'ai-k'ayin tafin k'afa da hannu, daga baya kuma sai abun ya canza, ta koma ciwon k'asusuwa, da zarar ta fara zazzab'i sai ko wace gab'a tata ta ringa mata ciwo, yanzu ko babu zazzab'in ma ciwo suke mata." Zare glasses d'inta ta yi ta ajiye daga gefe sannan ta hau dudduba Amrah, ta cire mata kaya. Tana cikin dubawar ba tare da ta d'ago kanta ba ta ce, "Me nene genotype d'in ki? (Sinadarin jini)" Pinky durling💗 *RAZ 2👌🏻* [8/30, 3:29 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 0⃣5⃣ Cikin mamaki na kalle ta, ina k'ok'arin tuna a inda ma na san kalmar, saboda na yi boko bakin gwargwado, sai dai ban yi zurfi sosai a ciki ba, daga JS 3 na tsaya ban samu damar ci gaba ba. Mahaifinta kuma ya gama secondary ne bai wuce ta gaba ba. "Me nene genotype d'in ki?" Ta sake tambaya ta bayan ta d'ago kanta ta kalle ni. "Dr. Ban gane nufinki ba." Na fad'a idona a cikin nata. "Sinadarin jini nake nufi. Wane iri gare ki?" Ta mayar da glasses d'inta. "Uhm...ni ma ban sani ba Dr. Kamar dai zan iya tunawa, sanda zamu zana jarabawar aji uku an auna mana jini, blood O gare ni." Na fad'a ina tunani. "Tabbas ma kuwa O ne, O negative in ban manta ba." Gyad'a kai likitar ta yi ta ce, "Ba shi nake nufi ba Maman Amrah, wannan ai type ne na jini (blood group), genotype nake nufi. An tab'a yi miki awo?" Sai a lokacin na gane manufarta. Na ce, "Gaskiya ba'a tab'a yi min ba Dr." "Subhanallahi!" Ta furta had'e da dafe kanta. "Ina mahaifinta yake?" "Yana waje ne, bari in kira sa." Na mi'ke tsaye. "Ku hanzarta please, daga ku ma na tashi aiki wani zai karb'e ni." Ta fad'a tana mai ci gaba da dudduba Amrah. Babu jimawa muka shigo ni da Mallam. Da sallama na ce, "Dr. Ga Mahaifin nata nan." D'ayar kujera ta sa na jawo sannan muka zauna, mik'o min Amrah ta yi na karb'a ta ce, "Mallam menene genotype d'in ka?" "Tab! Na dai san ko menene genotype saboda na karance sa a Biology shekaru da dama da suka gabata. Sai dai kuma babu abin da zan iya tunawa game da shi Dr. Ban wani tab'a yin gwajinsa ba. Lafiya dai ko?" Jinjina kai ta yi ta ce, "Gaskiya dole ku yo wannan gwajin, sai kun yi shi sannan zan sake duba ta. Ita ma yarinyar a yi mata, gobe sai ku dawo." Ta rubuta mana awon a wata takarda ta bani. "Ku gwada wannan takardar. Dan Allah ku tabbatar kun yi shi daga nan zuwa gobe." Mik'ewa muka yi sannan muka mata godiya muka fita. Bamu bar asibitin ba sai da muka binciki inda ake awon genotype, duka d'ari biyar aka caje mu mu duka ukun, aka ce sai zuwa gobe mu karb'i sakamako. A sa'bule muka nufi bakin asibitin, muna isa kuwa muka samu keke napep ta kawo wasu, babu b'ata lokaci ya d'auke mu sai gida. Bayan mun isa, a k'ofar gida muka tarar da Annur zaune ya yi tagumi, ya k'urawa k'ofar gidan ido. Sauka muka yi daga napep d'in muka sallame shi, sannan muka iso k'ofar gidan. Da sauri Annur ya mik'e, take bak'in cikin da ke bisa fuskarsa ya kau, ya karb'i Amrah daga hannuna. Murmushi na sakar masa na ce, "Annur lafiya dai ko?" Mallam ya yi saurin fad'in, "Yo sai ma kin tambaya? Bai ga 'yar lelen tasa ba ne yau." Ya ci gaba da zura makulli a cikin kwad'o yana k'ok'arin bud'e k'ofar. "Haka fa. Ai Annur ba nisa sosai muka yi ba. Mun je asibiti ne." Na fad'a ina masa murmushi had'e da shiga cikin gidan yana biye da mu. "Ai Umma da har hankalina ya tashi, na zata ko wani wurin mai nisa kuka tafi babu ko bankwana." "Ko kad'an Annur. Iyakacinmu asibitin Turai." Mallam ya fad'a. Bayan ya sauke Amrah tsaye ya ce, "Waye ne ba lafiya? Ko jikin Amran ne ya motsa?" D'aga masa kai na yi sannan na ce, "Amma kar ka damu, ta ji sau'ki sosai. An saka mu awon genotype ne, sai gobe zamu karb'i sakamakon mu kai ma likita." Dafe kansa ya yi, cikin lokaci kad'an yanayinsa ya sauya, idonshi ya yi jajur kamar wanda zai yi kuka, yana son yin magana amma lab'b'anshi sai k'yarma suke kamar ba zai iya ba. Ganin haka ya sa na 'kirk'iro murmushi na ce, "Annur miye ne haka wai? Babu wata matsala mai girma fa. Idan ma akwai, wayo da dabararmu ai ba zasu tab'a magance mana komai ba, addu'a kawai zamu rik'a, domin ita ce makamin mumini. Insha Allahu zata samu lafiya." Da k'yar ya iya furta, "Umma ina matuk'ar tausayin Amrah, bana so wani abu ya same ta. Jikina yana bani in har wata babbar matsala ce tattare da ita, to tabbas ni ma zan iya kamuwa da wata cutar. Ummah wallahi tausayinta nake ji..." sai a wannan lokacin hawayen da yake b'oyo suka samu nasarar fitowa. Ita kuwa Amrah kallonsa kawai take, ta dai san tabbas ba lafiya ba, ganin babban abokinta yana kuka..." Maryama ce ta yi saurin dakatar da Ummah da fad'in, "Kar dai na katse ki Ummah, baki fad'a min shi Annur d'in ko waye shi ba." Jinjina kai ta yi ta ce, "Haka ne Maryama. Annur Ikra Hussain shi ne asalin sunanshi. Mahaifin Annur babban mai kud'i ne, saboda a duk fad'in unguwarmu babu gida mai girman nasu, babanshi ya fi kowa kud'i, saboda tsohon pharmacist ne wanda ya jima da yin retire, yana da share a wasu daga cikin magungunan da ake yi, ciki kuwa har da kamfanin dana. Annur shi ne d'a na biyar a gidansu, duka yayyenshi mata ne, sai shi d'in ne kawai namiji, sai kuma k'anwarsa mai bi masa, auta ke nan. Yaro ne d'an kimanin shekaru sha uku a lokacin. Annur na da tarbiyya sosai, yana da son mutane, haka kuma akwai shi da girmama na gaba da shi. Mun had'u da shi ne tun wata rana a k'ofar gidansu, ni kuma mun je cike wani form na tallafawa mata, wanda mahaifiyarsa take kula da shi, kasantuwarta ma'aikaciyar gwamnati ce ta b'angaren state government. A lokacin Amrah na da wata biyar a duniya, shi kuma bai fi shekara goma sha d'aya ba. Tana ta tsala min kuka alamun ta gaji, shi kuma ya fito a inda muke jere a layi ya ji kukanta. Da sauri ya iso inda nake, ya kalle ni ya ce, "Me kika mata take kuka?" Har da nuna alamun shi ya ji haushi sosai. Murmushi na masa na ce, "Babu abin da na mata, rigima ce kawai. Ina ji ta gaji ne." "To ki mata yanda take so ko kuma na kai k'ararki wurin Babana, in fad'a masa kina ba 'yar yarinya wahala." Sosai ya bani mamaki, na d'aga kai na kalleshi, har a lokacin bai daina kallon Amrah ba. Na ce, "To ko zaka karb'e ta ka taya ni rarrashinta ne?" "Ehh kawo ta." Na kuwa mik'a masa ita. Duk irin kukan da yarinyar nan ke tsalawa, Annur na kar'barta ya ringa rirrigata ta yi shiru, k'arshe ma sanda ya dawo min da ita sai wangale baki take, kamar ba ita ce ta gama kuka ba. "Gata nan ta yi shiru. Ya sunanta wai?" Ya tambaye ni bayan ya mik'o min ita. "Sunanta Amrah." Na bashi amsa. "Ta burge ni. Ina ne gidanku? Zan ringa zuwa ina d'aukarta kullum idan tana kuka." "Gidan namu akwai 'yar tafiya yaro, ta can k'asa ne." Na gwada masa layin namu. "Sunana fa Annur ba yaro ba. Zan jiraki idan kin tashi tafiya sai mu tafi tare. Ina son Amrah, kaman ki bani ita ta dawo gidanmu." Ya kama latsa mata kumatu sai wangale baki take. Wannan shi ne silar had'uwarmu da Annur, tun daga wannan lokacin ya d'auki Amrah ya saka ta a ranshi, duk sanda bata lafiya haka zai wuni a gidan nan, idan tana kuka kuwa shi ma kukan zai yi, har sai sanda ta daina. Amrah ta matuk'ar sabawa da Annur, kamar yanda shi ma ya saba da ita sosai. Baya shigowa gidan nan ba tare da ya kawo mata wani abu ba, ta dalilin Annur har mahaifiyarsa ta zo nan gidan, ta kawo ma Amrah abun duniya iri iri, wai saboda yanda d'anta d'aya tal namiji ya nuna k'aunarsa ga yarinyar. Tarihin Annur Ikra Hussain ke nan. Bari mu koma mu ci gaba daga inda muka tsaya." Gyara zama Maryama ta sake yi tana mai sauraron Umma... Pinky durling💗 *RAZ 2👌🏻* [8/30, 3:29 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 0⃣6⃣ Umma ta ci gaba, "Ganin halin da Annur yake ciki, ya sa na ce, "Annur akwai Islamiyya fa yau, ka tashi ka tafi kar ka makara. Kuma ka share hawayen nan bana so ka tafi gida da shi." "Umma yau ba zan je Islamiyya ba, ko kin manta ke kika ce min daga asibiti kuke? Zan zauna har sai na tabbatar Amrah bata da wata damuwa daga nan zuwa dare, sannan zan tafi." Ya sake gyara zamansa. Mallam ya ce, "Ba za a yi haka ba Annur, gidanku ba zasu ji dad'i ka zauna a nan baka je makaranta ba. Mu ma kuma ba zamu so ta dalilinmu kana fashin makaranta ba. Ka tashi ka tafi ka ji? Gobe sai ka dawo ka duba ta, ka ga a lokacin ma an bata magani ta ji sauk'i ke nan." Ya sakar masa murmushi. Shi ma murmushin ya yi ya ce, "Kuma fa haka ne Abba. Bara in tafi to. Amrah.." ya kama mata hannu. "...zan tafi makaranta, zan fad'a wa Malaminmu a saka ki a addu'a, Allah Ya baki lafiya ko?" Murmushi kawai Amrah ta masa, ta ce, "Ameen." Ta san dai idan an ambaci addu'a to amin ake cewa, ita ma shi yasa ta ce haka. Sakar mata hannu ya yi, ya ce, "To sai Allah ya kai mu." "Allah Ya kai mu, Annur. Ka gaishe da Momy'nka." Na ce da shi. "Zata ji." Kawai ya fad'a tare da barin gidan. Na juyo ga Mallam na ce, "Wato k'aunar da yaron can yake ma Amrah, abin har mamaki yake bani. Yaron da bai yi ko shekara sha hud'u ba, amma ya ta'allak'a rayuwarsa ga Amrah, ya sadaukar da baki d'aya lokacinsa ga Amrah." Mallam ya jinjina kai ya ce, "Ai k'aunar da Annur yake ma Amrah, a jininsa take. Ki tuna ranar da Amrah ke ta kukan nan bata da lafiya, sai gashi fa da gudu ya zo, wai jikinsa ne ya bashi cewa Amrah na kuka bata da lafiya, kuma sai gashi hakan ne. Haka zai zauna ya rizgi kukansa idan bata da lafiya, sai idan ta yi shiru ko shi ma zamu samu ya yi shiru. Haka ita ma yarinyar, duk iya rigimar da take sai idan bai d'auke ta ba, tun ma kafin ta kai haka. Da zarar ya d'auke ta sai ta yi shiru. Ni tsorona d'aya ma, yanda iyayensa suke da kud'i, kar wata rana su wula'kanta mu saboda d'ansu, musamman yanda shi kad'ai gare su namiji, suna so su inganta rayuwarsa, amma wasu lokutan sai ya k'ek'ashe ya k'i tafiya makaranta saboda Amrah. Ina matu'kar tsoron ranar da abin zai cika su, zasu iya yin komai fa saboda Annur." Ajiyar zuciya na sauke, na ce, "Haka ne Mallam. Amma kuma fa son yaron nan da suke shi zai sa su masa duk abin da yake so. Ka tuna ranar da ya kawo Mamansa ta zo har nan ta duba Amrah? Alamun suna bayan buk'atarsa fa ke nan." "Allah dai Ya mana jagora." Kawai Mallam ya fad'a. "Da kin nufi d'ora abinci ai ko dan yarinyar nan, kafin ta nema." "Yanzu kuwa. Ai da yake mun yo cefane, d'orawa kawai zan yi." Na tashi na nufi d'ora girkin rana, a lokacin har la'asar ta kusa. Washe gari, Tun da sassafe muka gama shiri, takwas ma bata yi ba muka karya sai haramar komawa asibiti. Tun ba mu fita ba sai ga Annur ya zo, sanye yake da Uniform na Gobarau Academy, school bag goye a bayansa. Da fara'a ya ce, "Umma na zo duba Amrah ne, ta ji sauk'i sosai ko?" "Alhamdulillahi! Duk yau ko cikin dare ma bata yi ciwon komai ba. Ka ga shirin tafiya ma muke, asibitin zamu koma karb'an sakamako." Na bashi amsa ina tab'a kanshi. "To tun da ta ji sauk'i bari in tafi. Dama na matsa wa Baba Amadu ne lallai sai ya biyo da ni na duba Amrah. Bara in tafi, idan mun tashi zan biyo ko kun dawo lokacin." "To Annur, Allah Ya bada sa'a. Ka yi karatu sosai ka ji?" Ya jinjina kai had'e da fita daga gidan, a dai-dai fitowar Mallam daga d'aki ya rufe. "Kamar muryar Annur na ji ko?" Ya tambaye ni bayan ya datse d'akin. "Shi ne fa da kan shi. Wai ya zo duba mutuniyarsa ne." Na bashi amsa had'e da saka ma Amrah takalmanta. "Allah sarki!" Ya fad'a ya yi gaba na kama hannun Amrah, muka mara masa baya. Bayan ya rufe gidan, muka nufi titi, babu jimawa muka samu napep aka nufi Turai da mu. Ko da muka isa Turai child and maternity hospital, mun tarar da mutane sosai, kasantuwar akwai special doctor da yake zuwa a irin ranar ko wace talata, wanda musamman k'ananan yara yake dubawa. Kai tsaye laboratory (d'akin gwaje gwaje) muka nufa, mutum uku ne kawai a gabanmu, su ma kuma ba wai result suka je karb'a ba, sun je a yi masu wani awon ne na daban. Zama na yi bisa kujera na rungume Amrah, mallam kuma ya shiga ciki inda zai karb'o sakamakon. Bai jima ba sai gashi ya fito, ya ce in tashi mu tafi. Kusan minti arba'in muka d'auka kafin a bamu izinin shiga wurin likita, likitar jiya mai suna Dr. Xarah ce muka tarar, sai kuma wata d'aya likita zaune daga wata kujera, lab court ce a jikinta ta yi rolling d'in bular mayafi. Da sallama muka shiga, bayan mun gaisa ta ce, "Sannunku Maman Amrah. Ku zauna mana." Ta gwada mana kujeru guda biyun da ke fuskantarta. Zama kuwa muka yi, waccan d'aya likitar ta ce, "Dr. Xarah ni zan wuce, sai na gan ki." Dr. Xarah ta ce, "To shi ke nan Dr. Rabiatu. Insha Allahu zaki ji ni very soon. A gaishe min da yarana da Babansu." Bankwana suka yi sannan ta juyo gare mu, "Ina results d'in?" Ta fad'a bayan ta mayar da glasses a idonta. Mallam ya mik'o mun sannan na isar da shi gare ta, "Ga shi Dr." Na mik'a mata. Ta jima tana dudduba takardun, shiru ya biyo baya na tsawon minti sha biyar ko ma fin haka, kafin ta zare glasses d'inta ta ce, "Ya Salaam!"Ta dafe kanta. Bamu ce mata komai ba, sai dai ambaton sunan Allah da ta yi ba kad'an d'in razana ni ya yi ba, take na ji hankalina ya tashi, zuciyata na dukan uku-uku. Ajiyar zuciya nannauya ta sauke kafin ta ce, "Ban san me ya sa ba, abu mai matuk'ar muhimmanci amma mutane sam! Basu yarda da shi ba. Shekara da shekaru manyan likitoci sun sha fad'akarwa, cewa mu kasance masu awon genotype kafin mu yi aure. Ba wai ku iyayen ake ji ba, su yaran da zaku haifa d'in ne abun ji. Yaro k'arami, bai ji ba bai gani ba, bai san halin da duniya take ciki ba, amma tun yana k'arami a wargaza masa rayuwa, ta k'i yin inganci. Me yasa ba'a kula ne? Me yasa soyayya take rufe wa mutane ido su gagara aikata abin da ya dace? Shin mutane basa tausayi ne? Basa duba future d'in su? Su dai soyayya kawai, kar a b'ata ran masoyi. Yanzu fa wasu a tunaninsu da zarar na ce da wanda zan aura ya kamata mu yi awon genotype, zai iya daina so na ko? Zai iya ganin kaman ban yarda da shi ba ne? Zai ji a duniyarsa na raina masa hankali ko? Me yasa zaki zab'i faranta ran wani namiji, ki cuci yaron da zaki haifa? Ko kin san cewa matuk'ar hakan ta kasance, mijinki zai iya dakatar da haihuwa da ke saboda gudun wahala? Ko kin san cewa zai iya zuwa ya nemi mai AA ya aura, wacce zata ci gaba da haifa masa lafiyayyun yara? A rayuwar nan ta yanzu, wacce kud'i da lafiya suka yi k'aranci, kamata ya yi tun farko a gina rayuwa a kan abu mai kyau, a gina rayuwar yaro da tubalin mai kyau. Wallahi auren soyayya ba tare da bincika sinadarin jini ba, babu abin da yake haifarwa face wahala. Ba wai ga yaron kawai ba, har ku iyayen da zaku yita jerangwama da shi, kuna cikin damuwa. Yanzu ke baki sani ba, kin auri namiji wanda sinadarin jininsa AS ne, shi ma kuma ya aure ki, naki jinin AS ne, wane irin yara kike tsammanin zaku haifa? Idan masu sinadarin jini AS suka yi aure su duka biyun, akwai yiuwar fa su haifi yaro mai amosanin jini (sickler) Ba wai na ce lallai sai mai sickler zasu haifa ba, sai dai zasu iya samun sirkin mai sickler d'in. Zasu iya samun mafi rinjaye AS a cikin yaransu. Ita kanta AS d'in nan fa, akwai mai wahala, kafin ma a kai ga SS. Matuk'ar S d'in da ke cikin jininka ta rinjayi A d'in, to zaka iya zama mai laluri a ko da yaushe, tamkar yanda mai sickler zai yi, sai dai zaka iya samun sauk'i ba kaman na me SS d'in ba. Yanzu ku bayin Allah, kun san abin da rashin awon genotype ya haifar maku? Kun san cikin halin da kuka hefa 'yarku? Yanzu kai, kana da AS, Ita ma mamanta tana da AS, What do you expect? Kuna zaton zaku ci gaba da haifar yara lafiyayyu ne? Idan ma duka yaran naku lafiyayyu ne, kun san wanda zaku haifa a gaba? Ban ji dad'i ba ko kad'an, ku ne silar ciwon 'yarku, yarinyar da bata ji ba bata gani ba, jininta yana d'auke da amosani a cikinsa (sickle cell) a bisa sakaci da son zuciya irin naku. Duk ciwukan da kuka ga tana yi, wasu daga cikin illolin sickler ne, cutar yarinyarku ke nan...." ta dakata daga nan ita kanta cike take da tausayi, idonta kamar zai kawo ruwa. "...kuma duk irin wahalar da take tun tana da shekara d'aya, baku ta'ba tunanin kawo ta asibiti ba sai yanzu. Any ways, da sauk'i ma tun da kun zo yanzu d'in ai. Zan rubuta mata magunguna, sannan kuma akwai shawarwari da dama wanda in dai kuka bi su, insha Allahu cutar zata jima bata ringa tasar mata ba; Babban abin da yake tasar da ita shi ne malaria, saboda haka sai kun kula, ko da wasa kar ku ringa bari sauro na cizonta. Duk yanda zaku yi, ku tabbatar baku barta inda sauro zai cije ta ba. Akwai gidan sauro ana bayar da shi kyauta a ko wace asibiti, ku nema, da zarar magrib ta yi ku tabbatar kun saka ta a ciki, kar kuma ku bari sauron ya shiga a ciki. Abu na biyu, kar ku ringa barinta a cikin sanyi, saboda wannan sanyin zai iya saka mata zazzab'i, kuma zazzab'in masu sickler shi ne wanda ba a so. Saboda su basu iya zazzab'i ba, da zarar sun fara shi zai iya k'onar masu da baki d'aya jininsu, idan ma ba a hanzarta an saka masu wani ba, zasu iya rasa rayuwarsu. Abu na uku, banda duka. K'ashinsu ba wani k'wari ne da shi ba, da zarar kun duke ta, zaku iya tab'o inda bai dace ba, kuma k'arshe wahalar ta dawo a kanku. Hakan kuma ba wai yana nufin kar ku tarbiyyantar da ita ba, a'a, sai dai ku kula. Ku san ta hanyar da zaku bi idan ta yi laifi. Ko School ta shiga nan gaba, ko da wasa kar ku bari ana dukanta. Pinky durling💗 *RAZ 2👌🏻* [8/30, 3:30 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 0⃣7⃣ Abu na hud'u, ungo wannan." Ta jawo wata lakar gabanta, wani abu ta zaro sannan ta mik'o min, "Thermometer ce wannan. Duk sanda zazzab'i ya kama ta, komai k'ank'antarsa ku ringa amfani da wannan, zaku saka a armpit d'inta, matuk'ar kuka ga ya kai 37.5degreeC, ko kuma idan a baki kuka saka mata, ya wuce 38degreeC, to lallai ku hanzarta ku kai ta asibiti mafi kusa da ku, saboda ya riga da ya haura, ya kai minzalin da zai iya k'one mata baki d'aya jininta. Amma idan kuka kawo ta, sai a d'auki mataki tun da wuri kafin abun ya yi nisa. Abu na biyar, shi ne folic acid. Ya zamana kullum kuna bata folic acid, ko kad'an kar ku ringa mantawa, zai bada taimako sosai da sosai. Na shida, ta yawaita shan ruwa, ba kuma wai ruwan sanyi ba. Ruwa sosai zaku yawaita bata, saboda shi dama ruwa waraka ce ta cututtuka da dama, not only sickler. Da zarar tana shan ruwa wadatacce, zaku ga tana fitsari akai akai, wannan fitsarin nata sauk'i ne sosai. Da zarar kuwa bata fitsari sosai, to lallai akwai damuwa, dole zaku kawo ta asibiti a duba ta. Wannan su ne abubuwan da ya kamata ku kula, ku tabbatar kun fita hak'k'inta, in har kuka aikata kaf abubuwan dana lissafa maku, lallai zata kasance mai cutar sickler amma sauk'ak'k'a. Abu na k'arshe, ku ringa mata addu'a, saboda ita addu'a takobin mumini ce. Sannan kuma kafin a saukar da cuta, sai da aka saukar da maganinta. Allah maji kan bayinSa ne, mai karb'ar addu'ar bayinSa. Ku ja yarinyarku a jiki, ku nuna mata soyayya, ku inganta abin da ya yi saura na rayuwarta, bakin gwargwadon iyawarku." Dr. Xarah ta yi shiru daga nan cike da tausayi. Sosai kuka ya ci k'arfina, Mallam ne kawai mai d'an kuzari, shi d'in ma da zarar an ganshi an san damuwa na tattare da zuciyarsa. Murmushi ta k'irk'iro ta ce, "Maman Amrah sai hak'uri, Allah'n da Ya d'aura mata cutar shi zai bata sau'ki. Ba kuma wai dan ba Ya sonta ba ne, a'a, jarrabta ce, kuma babu wanda ya fi k'arfin Allah Ya jarrabce sa. Masha Allah, yarinyarku kyakkyawa da ita, gata b'ul-b'ul babu wanda zai kalle ta ya ce sickle cell ce. Abin da ya rage, kawai ku yawaita bata abinci masu gina jiki, insha Allahu ba za a ta'ba ganewa ta jikinta ba. A shawarce, saboda gaba, duk wanda zai nunar da yana sonta, ko ba dad'e ko ba jima, kar ku b'oye masa cutarta. Saboda tun da wuri in ma bai san genotype d'insa ba sai ya nemi sani, idan har AS gare shi, duk irin son da yake mata dole ya hak'ura. Idan kuma Allah Ya sa AA ne da shi, kun ga shi ke nan." Nannauyar ajiyar zuciya na sauke, na ce, "Mun gode k'warai Likita. Insha Allahu zamu bi shawarwarinki, Allah Ya saka miki da alkhairi. Amma likita, hakan ko yana da nasaba da mutuwar da yaranmu suke yi idan mun haihu? Amrah ce yarinya ta uku da muka haifa, sauran biyun duk sun rasu." Dr. Xarah ta ce, "Tabbas ma kuwa, hakan zata iya kasancewa. Saboda wasu yaran idan nasu mai tsanani ne, ba a ma ganewa sai dai mutuwarsu kawai. It can be possible, mai tsananin ce tun wuri sai Allah Ya d'auke su." Shiru na yi kad'an ina nazari kafin na ce, "To shi ke nan. Fatanmu dai, Allah ya sau'kak'a wa duk musulmin Allah." "Ameen. Idan kun fita sai ku nemi inda ake rijistar masu sickler, kyauta ake bayar da magungunansu a nan asibitin. Duk bayan sati biyu sai ku ringa zuwa kuna karb'ar mata." Ta dafa kan Amrah, "Amrah! Sannu kin ji? Allah Ya baki lafiya. Ki ringa yi wa kanki addu'a ko?" Ta sakar mata murmushi. Murmushin na k'irk'iro na ce, "Insha Allahu zan ringa saka ta tana ma kanta. Bari mu tafi. Mun gode k'warai." Muka mik'e. Har a wannan lokacin Mallam bai ce komai ba, damuwa fal a fuskarsa. Ba mu bar asibitin ba, sai da muka mata rijista, aka bata magungunan wannan satin, sannan muka tafi. K'arfe sha biyun rana ta wuce sanda muka isa, ta yi bacci hakan ya sa na kwantar da ita, sannan na nufi d'ora girkin rana. Bayan azahar, sai ga Annur ya zo, hannunshi rik'e da launch box d'insa, bayansa kuma goye da jikarsa. Da fara'arsa ya k'ariso inda take zaune, zama ya yi shi ma ya ce, "Amrah..." ya bud'e launch box d'in ta shi. "...ga sauran abincina nan na kawo miki. Ban cinye ba saboda ke..." Ya ajiye a gabanta, sannan ya bud'e jikarsa, "...wannan kuma chocolate ce na siyo miki. Kar ki ba kowa." Ya fara bud'e mata ledar. Daga inda nake na saki murmushi, sannan na iso inda suke. "Wato dai Annur mu kake nufin kar ta ba ko? Ka yi dai-dai to." Mallam da ke zaune ya murmusa ya ce, "Ahh to, mu ma idan mun samu na mu sai mu hana su ai." "Umma an karb'o result d'in nata kuwa?" Ya tambaye ni. Zama na yi kusa da shi, na ce, "An karb'o, Annur. Amrah sickler ce da ita." Na yi saurin share hawayen da ya fito min. "Sickler Ummah? Irin wadda Saddam yake da ita? Gaskiya k'arya ne. Shi fa jikinshi babu girma, sai aukin k'ashi kawai. Babban kai kuma da shanyayyun k'afafuwa gare shi. Shi ne kuma za a ce wai Amrah ita gare ta? Ummah ko dai 'karya likitan yake maku?" "Waye Saddam?" Na tambaye shi. "Wani abokina ne. Sanda muna JS2 ma ya rasu." Ya bani amsa cike da damuwa. "To ai ka ga shi da Amrah ba d'aya ba. Ita wannan cutar dama kowa da yanda take zo masa. Wani da sauk'i, wani kuma babu sauk'i. Akwai wanda take canza ma halitta, kaman yanda ka ce ta Saddam d'in. Ita kuma Amrah, ka ga ta ta mai sauk'i ce, sai mu gode wa Allah ke nan, tun da abun ya zo da haka. Kar ka damu Annur, insha Allahu babu wata damuwa, Allah Yana tare da mu, kuma shi zai bata lafiya. Kai dai kawai abin da nake so da kai, ka ringa saka ta a addu'a, kar ka fasa. Zata samu sau'ki kaman kowa." Na sakar masa murmushi. "To shi ke nan Umma. Zan ringa yi mata addu'a har ta samu sauk'i." "Yauwa d'an al-barka, yanzu ka tashi ka tafi, ka huta kafin lokacin Islamiyya ya yi." Mallam ya fad'a bayan ya dafa masa kai. D'aure fuska Annur ya yi, ya ce, "Ni fa yau ba zan tafi ba, zan zauna a nan sai dare sannan. Har ma na sallami baba Amadu tun d'azu ya tafi." Cike da mamaki na ce, "Wace irin magana kake yi Annur? To me zaka zauna ka yi a nan? Na ce maka Anrah ta ji sauk'i fa. Ka tashi ka tafi kar Mommy ta maka fad'a." Fir fir yaron nan ya ce ba zai tafi ba, shi fa yana nan zai yi jinyar Amrah ta yau. Kumci na dafe, na ma rasa abin da zan yi. Mallam cikin dabara ya ce, "To ka tafi gida, ka ciro uniform d'inka sannan ka dawo, sai ka yi jinyar ta ta. Amma a haka, ai babu dad'i zama da uniform." Ya masa murmushi. Fuska ya sake tsukewa, yana neman yin hawaye ya ce, "Shi ke nan bara in tafi, tun da dai kora na kuke daga gidanku." Sai ga hawaye sun fara masa sintiri a kumatu. D'aukar launch box d'insa ya yi, da jikarsa, yana kuka ya kama hanyar tafiya. Baki d'aya na ji zuciyata ta yi sanyi, ba zan iya barinsa ya tafi a haka ba, hakan ya sa na jawo sa, na ce, "Yi ha'kuri yarona. Tun da baka son tafiyar, zauna abunka ka ji?" "Umma ba dai ni kuke kora daga gidanku ba? Shi ke nan ma, ba zan sake zuwa gidanku ba." Ya fizge hannunsa da na rik'e. Da hanzari Mallam ya kamo shi, da fara'a ya ce, "Zo nan abunka. Ka yi hak'uri ka zauna ka ji? Ko dan Amrah, ka ga har ta fara kuka." Kallon Amrah ya yi, ganin da gaske kukan take ya sa ya dawo da sauri, ya hau bubbuga bayanta yana bata hak'uri har ta yi shiru. Daga nan suka hau wasansu, yana ta bata labarin makaranta, ita kuwa murmushi kawai take, dan bata san abin da yake fad'a ba. Ko da abinci ya dahu, tare na zubo masu shi da ita, yana bata a hankali a baki. Sai da ya tabbatar ta k'oshi, sannan shi ya fara ci. *K'ARFE HUD'U DA RABI NA YAMMA (4:30PM)* Pinky durling💗 *RAZ 2👌🏻* [8/30, 3:30 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 0⃣8⃣ Wata budurwa ce ta shigo, hannunta rik'e da wata yarinya, wadda kallo guda zaka mata ka tabbatar ta had'a jini da Annur. Babu ko sallama suka shigo, biye da su wani matashi ne, sanye da matattun kaya, wanda na tabbatar cewa d'an koransu ne. Tafe suke yana masu jinjina, had'e da kirari tamkar ya ga manyan Al-hazai. Ko da ganinsu, tuni Annur ya mik'e tsaye, mamaki fal a fuskarsa ya ce, "Aunty Saddiqa." Tabbatarwar da na yi cewa danginsa ne, ya sa da fara'ata, duk da yanayinsu da na gani, cike suke da izza da gadara, na ce, "Lale marhabun da ku. Ku iso ga tabarma ku zauna." Kallon uku saura kwata Saddiqa ta bi ni da shi, bata ce min komai ba, sai dai ta kalli Annur cike da masifa ta ce, "What's wrong with you, boy? What are you doing here?" Ta sake bin gidan da kallo a k'ask'ance, "Wai me kake tsinta a gidan nan ne? Lukkat the floor..." ta nuna k'asa da hannunta, alamun k'yama, "...a haka kake zaune, har kuma kake iya had'iyar yawu? Taso maza mu tafi, tun ban mammare ka ba." Iya 'kuluwa na k'ulu, bana son raini da wulak'anci, musamman ma yanda ta zo har inda muke ta same mu, kuma take neman wula'kanta mu. "Ya Noor abeg let's go mana. Lukkat your uniforms, duk sun yi k'ura saboda floor d'in gidan, amma a haka kana zaune, ji k'azamar yarinyar da kake wasa da ita..." ta nuna Amrah. Tun bata rufe bakinta ba, Annur ya hanzarta isa inda ta ke, ya mata wani mugun kallo, kafin ya ce, "Islam, mind your tongue. Da ki tab'a Amrah, gwara ni ki yi min. Wai me ma...?" Bai gama maganarsa ba, ya ji sautin tsawar da Saddiqa ta masa, "Shaarrup your mouth Noor! K'arya Islam ta yi ne? Kullum kana fama da zuwa gidan da bai kamace ka ba, kana k'ok'arin gurguntar da rayuwar iliminka, a maimakon ginuwar da iyayenka suke maka. Me yake damunka? Me ya sa ba zaka fita harkar mutanen da basu cancanta.." "Ya ishe ki haka!" Na fad'a a fusace. K'arisowa na yi inda take, cike da takaici. Iya k'ok'ari na yi shi, na so a ce na iya daurewa, na k'yale ta. Amma ina, sam! Na ji zuciyata ba zata iya d'auka ba, ba zan iya jurar cin fuskar da Saddiqa take min ba. "Na kula, duk girmamawar da na miki, ko kad'an ke baki ga hakan ba. Na kula, sam! Baki cancanci darajta kin da na yi, saboda Annur ba. A rayuwata, bana son cin zarafi, da kuma cin fuska. An fad'a miki tsoro ne ya sa ni yin shiru, bayan duk cin fuskar da kike min? Wa ya fad'a miki shiru-shiru tsoro ne? Ko kuwa an ce miki talauci hauka ne? A tunaninki bamu da wata daraja ne, saboda muna talakawa? Annur da kike gani, ban tab'a jawo shi na ce ya zo inda muke ba, ban tab'a kiransa da sunan ya zo gidan nan ba. Dan Allah na ro'ke ki, ki tafi ki bar mana gida. Duk iya talaucinmu, mun rik'e shi, bamu fita yawo kwararo kwararo muna maula ba. Ki fita, tun ban tara miki mutanen anguwa da sunan kin zo har gida, kina tak'ulana da fitina ba. Na rok'e ki, ki kama k'aninki, ki kuma shaida masa, ya tsaya inda Allah Ya ajje sa. Dan na ga alama, zuwansa inda muke, babu abin da zai jawo mana, face b'acin rai. Ki tafi kawai!" Na nuna mata k'ofa, gabana sai dukan uku-uku yake. Hankalina a tashe yake, ko kad'an bana son fitina, bana son ana fitina a inda nake. Wata irin muguwar dariya ta fasa, tana tafa hannuwanta. Wannan gardin wanda suka zo da shi, ya bud'e baki zai min masifa ta yi saurin dakatar da shi. "Barta!" Ta juyo gare ni. "Ki fad'i komai Madam, its your time." Ta had'a babbar yatsarta, da yatsar tsakiya, na hannun damanta ta murza su da k'arfi, har sau uku. "Zaki san kin fad'a min bak'ak'en maganganu. Ba dai ni ba? Hmm!" Islam cike da rashin kunya da fitsara ta ce, "Matsiyata kawai. Ji yarinyar ma kayanta duk sun tsufa. Gashin kanta ko gyara babu. Lukkat everywhere..." ta hau yatsina tana kalle-kallen ko ina dake cikin gidan. "Aunty Saddiqa mu yi mu tafi, dan kr wata cutar ta kama mu Please." Ta hau dod'e hancinta. Tuni Annur ya d'auke ta da mari, sai faman huci ya ke, ya ce, "Wallahi Islam idan na sake jin bakinki, sai na kakkarya ki." "Ni kuma in b'ab'b'alla ka ba. Ai gaba da gabanta." Saddiqa ta fad'a. "And ka zo mu tafi, tun ban maka da k'arfi da yaji ba." Rai a b'ace, ya juyo ya kalle ni. Sosai hankalinshi ya tashi, ganin yanda damuwa ta dabai-baye duk ilahirin fuskata. Ya duk'a daf da Amrah, murmushi ya k'irk'iro mata, ya ce, "Zan tafi Babyna. Please don't cry. Gobe da sassafe kafin in tafi School zan biyo in sake duba ki. Yi min dariya ko?" Dariyar kuwa ta yi, sai dai ganin ya mik'e tsaye alamun tafiya zai yi, ya sa ta fasa kuka mai k'arfin gaske. Yana k'ok'arin komawa mazauninta, da 'karfi Saddiqa ta finciko sa, har sai da ya kusa buguwa da bango. "Wallahi Annur, idan baka zo mun tafi ba sai na ci mutuncinka." Babu yanda ya iya, a haka ya bi bayan yayarsa da kuma k'anwarsa, yana yi yana waigen Amrah, da har yanzu take kuka kamar ranta zai fita. Sai da suka tafi, na ji wani irin kuka wanda ba zan iya tsayar da shi ba, zafafan hawaye ke fita daga k'wayar idanuwana, wanda zan iya kiransu, da hawayen takaici. Wuri na nema na zauna, ina mai ci gaba da ruwan hawaye, ga Amrah ma bata yi shiru ba. Muna cikin hakan, sai ga Mallam ya shigo, biye da shi, k'aninshi ne mai suna Marwana. Da sallama suka shigo, na amsa ina mai k'ok'arin tsayar da hawayen da har yanzu suka kasa tsayawa, had'e da jawo hab'ar zanina ina share wanda suka gama wanke min fuska. Duk da k'ok'arin da na yi dan ganin na b'oye damuwata, hakan bai hana su Mallam fahimtar halin da nake ciki ba. Da azama Mallam ya iso inda nake, fuskarsa ta nuna damuwa k'warai da ainun. "B'oye damuwa sam bata cancanta a bisa fuskar da ruwan hawaye ya gama wankewa da ita ba. Halin jarumta, sam! Bai cancance ki a dai-dai wannan lokacin ba. Ko mutum bai sanki ba a baya, idan har ya kalle ki a wannan lokacin, sai ya tabbatar da lallai kina cikin damuwa. Ki fad'a min Murjanatu, wane irin abu ne ya faru da ke, wanda har ya saka ki kuka? Da alama dai ba ciwon Amrah ba ne, saboda ba haka zan same ta ba idan har shi d'in ne. Yanayinku ke da ita, ya tabbatar min da cewa wani abu ne, wanda a tare ya b'ata maku rai." Ya dakata daga nan, yana mai k'ok'arin zama a kusa da ni. Marwana kuma, ya d'auki Amrah yana ta rurrugarta, har ya samu nasara ta yi shiru, babu b'ata lokaci, cikin mintunan da basu fi biyar ba, bacci ya d'auke ta. Nannauyar ajiyar zuciya na sauke, na kalli Mallam na ce, "Mallam ashe talakan da yake zaune inda Allah Ya ajje sa, ya rik'e talaucinsa, zai iya zama mai laifi ga masu wadatar dukiya? Ashe rashin shiga shirgin wasu, zai iya jaza mana wata matsala, ga wanda suke ganin sun fi mu d'aukaka? 'Yan uwan Annur ne suka zo..." na fad'a masa duk yanda muka yi da su har sanda suka tafi. Cikin nuna halin ko in kula Mallam ya ce, "To kuma shi ne ya zama abun damuwa da har kike asarar ruwan hawayenki? Ni a ganina, ko kad'an wannan ba zai iya zama silar b'arnar hawayenki ba. Ai da sauk'i, tun da ba gidansu kika je da nufin neman taimako ba. Har cikin gidanki suka same ki. To sai me?" Gyad'a kai na yi, na ce, "Amma Mallam, baka ganin abin da suka min tamkar cin fuska ne a gare ni? Duka a shekaru, Saddiqa ba zata wuce shekara goma sha tara zuwa ashirin ba. Islam fa? Ko goma ban ce zata yi ba. Amma a haka suka ringa cin zarafina, suna fad'a min magana, tamkar talauci hauka ne." Hawaye ya sake cin k'arfina. "Haba Murjatu! Yanzu ke, yarinyar da ba zata wuce shekara ashirin ba ce ta sa kika zauna kike kuka?" Marwana ya kwantar da Amrah bisa tabarma, ya ce, "Yaya Abdallah, dole Maman Bilal (Sunan da dangina da na Mallam suke kirana da shi, tun sanda na haifi yarona na farko mai suna Bilal, kuma har ya rasu basu daina kirana da shi ba.) zata yi kuka. Abin da kake ganin bai kai ya kawo ba, yarinyar da ta yi k'anwa ta biyar da ita, amma ta tsaya tana fad'a mata maganganu, tana mata rashin kunya. Wallahi, Allah ne Ya kyauta. Da a ce na tarar da su, suke mata fitsara, da duk abin da zai faru sai dai ya faru. Dan wallahi marin yara zan yi, in yaso sai mahaifin nasu, Alhaji Iqra Al-Hussein ya sa a d'aure ni, a kashe ni." Mallam ya ce, "Sai hak'uri ai. Komai na duniyar nan, sai ana kai zuciya nesa. Wata rana sai labari." "Haka ne." Na fad'a had'e da share hawayena. Pinky durling💗 *RAZ 2👌🏻* [8/30, 3:31 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 0⃣9⃣ Jinjinar ban giram ga 'Yan *RAZ NOVELLA.* Fatan alkhairi a ko da yaushe. Na gode da k'warin guiwar da kuke bani. Keep it up dearies.❤ *** Haka dai muka yi yammacin wannan rana, baki d'aya rayukanmu, sun yi bak'i k'irin. Hankulanmu sun dagule. Ko da dare ya yi, na ke ma Mallam magana cewa, "Ni ina ga kaman mu dakatar da Annur daga zuwa gidan nan, hakan ne kawai zai saka mu a cikin kwanciyar hankali. Ba zata yiu a ce saboda shi ana cin zarafinmu ba, k'aramar k'anwata tana fad'a min magana son ranta." Mallam ya nisa, ya ce, "Hakan da kika fad'a sam! Ba shi ba ne mafita. Idan Annur ya zo gidan nan, korarsa zamu yi? Kina ga kamar mun masa adalci idan muka hana shi zuwa inda muke? Annur yaro ne har yanzu, wanda bai mallaki hankalin kansa ba. Ya kamata mu masa uzuri, tun da ba shi ya miki ba, hasali ma, shi kanshi bai ji dad'in lamarin ba. A ganina, idan har ya zo muka dakatar da shi daga zuwa, ba mu kyauta masa ba. Ki duba ki ga sha'kuwar da ke tsakaninsa da yarinyar nan, ki ga halin da yake shiga duk sanda bata da lafiya. Kina ganin mun masa adalci idan muka raba shi da ita a lokaci guda?" Share hawayen da suka zame min abinci, a duk yammacin ranar na yi, na dube shi, na ce, "Mallam wannan fa abu ne wanda ya shafi martaba da mutuncinmu. Matuk'ar muka bar yaron nan yana ci gaba da zuwa, bamu san me gaba zata haifar ba. Idan yanzu yayarsa d'aya da k'anwarsa ne suka zo, gobe bamu san wa zai zo ba. Wata k'ila mahaifiyarsa da mahaifinsa ne zasu zo. Amma idan muka hak'ura da shi, shi ma sai ya ha'kura da Amrah, tun da dama tun asali bai santa ba bata sanshi ba. Kowa sai ya zauna a inda Allah Ya ajje sa." "Gaskiya kika fad'a Murjanatu. Sai dai kuma fa ni ba zan ta'ba iya korarsa idan ya zo ba. Zan dai bar miki wannan aikin, sai ki san yanda zaki yi da shi." Daga nan ya gyara kwanciyarsa, ya tofa addu'ar bacci. Ni ma kwanciyar na yi, amma fir-fir bacci ya k'i d'auka ta. Da zarar na runtse idona, sai in tuna abin da Saddiqa da Islam suka mana. Da zarar na fara tunanin yanda zan hana Annur zuwa, sai wata zuciyar ta nusar da ni darajar hak'uri. Baki d'aya sai in ji zuciyata ta yi sanyi, ba zan iya tsayar da shi ba. Ko ba komai Annur ya gama min komai, ya nuna tsantsar soyayyarsa ga gudan jinina, ya d'aura damuwarsa a kanta, ya sadaukar da lokacinsa a kanta. Na masa adalci idan na raba su? Ita kanta Amrah, na mata adalci idan na tsayar da farin cikinta daga zuwa inda take? Kuka sosai nake, wanda na kasa tsayar da su, na kasa tantance ko na menene. Shin, na damuwar abin da ya faru ne? Ko kuwa na tausayin halin da Annur da Amrah zasu shiga idan suka daina ganin junansu ne? Na sani sarai, ta Amrah mai sauk'i ce. Akwai yarinta a tattare da ita, ba zata jima ba zata iya mancewa da shi. Shekara d'aya ma idan ta d'auka bata ganinsa, zata manta da halittarsa a doron k'asa, matuk'ar ba maganarsa nake mata ba. Shi kuma fa? Zai iya mantawa da ita? Ko kuwa zai iya cire k'aunarta daga zuciyarsa? Kaina na dafe, had'e da had'iyar yawu da k'yar, na mi'ke tsaye. Ko da na duba tsohuwar agogon da ke jikin bango, k'arfe sha biyu da rabi na dare ne. Fitila na kunna, sannan na fita daga d'akin. Ban-d'aki na nufa, na d"auro alwala sannan na dawo cikin d'aki, na hau jera sallolin da ko ni ban san adadinsu ba. Ba ni ce da tashi ba sai kusan k'arfe ukun dare, sannan na hau gado, babu jimawa bacci ya d'aukeni. Washe gari da safe, ina ta tsammanin zuwan Annur kamar yanda ya fad'a, amma sai bai zo ba, har goman safe ta wuce. Ban yi mamaki ba, dan na san dama ba lallai ba ne ya zo, duk kuwa da yanda ya so zuwa d'in. Abu wasa ba wasa ba, har aka yi sati biyu babu Annur babu alamunsa. Tun abun baya damu na, har na fara damuwa. Amrah kuwa, sunan da na koya mata take kiransa da shi, take yawan fad'i cike da damuwa, "Hamma!" Take fad'i dare da rana. Wani lokacin tana kuka, wani lokacin kuwa har hijabina take d'aukowa tana bani, tana fad'in sunan Hamma, manufarta wai in kai ta inda yake. Shi kanshi Mallam abin ya dame shi. Ranar da Annur ya cika sati biyu bai zo inda muke ba, ya same ni da maganar, a tsakar fida da wani yammaci, "Raina yana matuk'ar b'aci, zuciyata tana yamutsa, kaina yana dagulewa, a duk sanda na tuna da yaron nan. Ban san me ya sa ba, ina jin rashinsa har cikin zuciyata. Ina k'aunar Annur, ina tsannain kewar rashin zuwansa gidan nan. To ni ma ke nan, ina ga Amrah? Ya take ji? A haka kuma dole ta bar abin a ranta, saboda yarintarta." Baki d'aya jikina ya yi sanyi da kalamansa, ni kaina ina jin rashinsa har cikin raina, musamman ma idan Amrah na kuka, tana nemansa. "Mallam ban san..." na dakata daga nan, saboda tozali da idanuwana suka yi da wanda muke kan maganarsa. Da sauri Amrah ta ruga ta isa gare shi, ta rungume shi sosai kamar wani zai k'wace mata shi, tana fad'in, "Hamma..." sai kuma ta yi shiru, ta sake kallonshi ta k'yalk'yale da dariyar da ke nunar da tsantsar farin cikinta. A yanayinsa, dole mutum zai fahimci damuwar da yake cikinta. "Sannu Annur." Na fad'a ina masa murmushi. "K'ariso ka zauna mana Annur, zo ga tabarma nan." Mallam ya fad'a tare da gwada masa kusa da shi. Zama ya yi yana d'auke da Amrah, ya gaishe mu. "Kamar kana cikin damuwa, lafiya dai ko?" Na tambaye shi. "Umma akwai damuwa..." ya fashe da kuka mai tsuma zuciya, wanda har sai da ya karya min zuciya. "Daddy'na ya ce zai mayar da ni Cyprus, inda Aunty Nadrah take aure. Su Aunty Saddiqa ne suka kai masa zuga, wai bana karatu, kuma bana zuwa School, kullum wai ina nan gidan, wurinku. Dady'na mutum ne mai son ilimi, yana son mu yi zurfi a karatu. Hakan ya sa ya yanke hukuncin tura ni can wurin yayata, wai in ci gaba da karatu a can, har lokacin da zan mallaki hankalin kaina. Mamana kanta hakan bai mata dad'i ba, saboda yanda ta kula da bana so, ita kuwa tana son abin da nake so." Ya yi shiru daga nan, saboda kukan da ya ci k'arfinsa. Da k'yar ya iya ci gaba da, "Bana son rabuwa da Amrah, na so na kasance tare da ita, na kula da ita ko dan ciwon da take tattare da shi. Na so a ce ta girma a gabana, in kula da ita, in k'aunace ta kamar yanda yayanta na jini zai mata. Sai dai kuma kash! Hakan ba mai yiuwa ba ne, an b'ata min tsarina a kan yanda na so gina rayuwata." Ya share hawayensa da hab'ar rigarsa, sannan ya ci gaba, "Ina son Amrah, Ummah. Bana son abin da zai raba ni da ita. Ina so ku min wata alfarma guda d'aya, wacce in har kuka min ita, kun gama min komai." Cikin kuka na ce, "Ina jin ka Ann..nur.." na yi k'ok'arin shanye kukan da ke son hana ni magana. "Kasantuwar Amrah yarinya ce, wacce babu wuya zata iya mantawa da ni. Ina son ku yi bakin k'ok'arinku, na ganin bata manta da ni ba. Na sani abu ne mai wahalar gaske, amma ina son ku min wannan alfarmar." Cikin k'arfin hali da nuna jarumta Mallam ya ce, "Na maka wannan al-k'awarin, Annur. Da yardar Allah Amrah ba zata tab'a mantawa da kai ba. Zata sanka ko da ba a baki ba, a suna ma kawai. Zamu ringa k'ok'arin sanar da ita irin halaccin da ka mata a yarintarta." Sallama muka ji, muryar wani dattijo ne. Mallam ya amsa sallamar had'e da mik'ewa yana shirin fita. "Annur baku gama ba? Har Yallab'ai ya kira ni yanzu, na ce masa motarmu ce ta d'an tsaya." Mutumin ya fad'a da d'an k'arfi, yanda Annur zai ji. "Ina zuwa Baba Amadu." Ya kama hannuwan Amrah duka biyun, kuka sosai yake, kamar wanda aka duka. Ita ma Amran kaman ta san abin da yake faruwa, ta dai gan ni ina kuka, ga kuma babban abokinta ma yana yi. Kukan take sosai kamar ranta zai fita. "Ina k'aunarki Amrah. Ban so a raba mu ba a dai-dai wannan lokacin. Na so na kasance tare da ke, na so na kula da lafiyarki, amma Allah bai nufa ba. Dan Allah Amrah kar ki manta da ni, kar ki manta da Annur Iqra Al-Hussein a rayuwarki. Ga wannan, kud'ina ne da abokin Dady'nmu ya tab'a bani sanda na je gidansa kwanakin baya, babu wanda ya san da su, ko Momy'nmu kuwa. Ina ta ajiyarsu ne, kamar na san abin da zai faru. Naki ne halak malak, duk sanda wata buk'atarki ta taso, tun daga kan magani har sutura, a miki amfani da su." Ya zaro rafar dubu d'ari daga cikin wata bak'ar leda, ya damk'a ta ga Amrah. "Na tafi. Sai wata rana.." kuka ya ci k'arfinsa. Da gudu ya bar gidan, mallam na k'iransa amma ko waigowa bai yi ba. _My fans, how was this chapter? Very touching ba? Soyayya ke nan. Comments d'inku yana 'kara min k'warin guiwa a ko wane lokaci. Amrah loves you irin over d'in nan.😍_ share to your friends Pinky durling💗 *RAZ 2👌🏻* [8/30, 3:31 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 1⃣0⃣ Wani irin kuka na fasa tamkar k'aramar yarinya, wanda duk jarumtar Mallam kasa bani hak'uri ya yi, shi kan shi kukan zuci yake, wanda a fuska kawai zaka iya fahimtar haka. Jawo Amra da ke kuka kamar ranta zai fita na yi, na d'ora a cinya sai faman rurrugarta nake. Cikin kuka na ce, "Ki yi ha'kuri Amrah. Duk da ba lallai kin san abin da yake faruwa ba, sai dai na san dole jikinki zai baki, rashin masoyinki na gaskiya. Annur ya tafi ke nan, bana tunanin zai sake waiwayarki. Ba wai ke kad'ai ba, ni kaina cike nake da zullumin kewar Annur da na tabbatar sai na yi ta. Sati biu kawai da ya yi bai zo ba, ji na yi kamar in bi shi. Gashi yanzu zai yi tafiyar da ba lallai na sake ganinshi ba. Tabbas Annur yaro ne d'an halak, wanda samun kamarsa zai yi matuk'ar wahala a dai-dai wannan lokacin. Shekararsa goma sha uku, amma halayensa kamar sun fi na yawan mai shekarun nasa." Na kuma fashewa da wani kukan, zuciyata sai tafarfasa take, ina jin kamar na kira Annur ya dawo gare mu, kamar na hana sa wannan tafiyar. Sai dai kuma bani da yanda zan yi, domin kuwa k'addara ta rigayi fata. Hukunci ne wanda mahaifinsa ya yanke, bani da yanda zan yi face hak'uri. *BAYAN SHEKARA TAKWAS* A dai-dai wanan lokacin ne Amrah ta cika shekara goma a duniya. A iya tsawon wannan shekaru, wahala iya wahala tana yinta, saboda baki d'aya yanda muka d'auki sickler d'inta ba haka ba ne. Wahala sosai take bata, ashe irin mai tsananin nan ce da ita. Kullum cikin zarya asibiti muke, tun muna damuwa, har Allah Ya saka mana tawakalli a zukatanmu. Ita kanta yarinyar, ta saka ma ranta dangana. Ranar wata laraba, da yammaci, misalin k'arfe shida na yamma, Da gudu Amrah ta shigo, har tana cin tuntub'e. "Umma.." ta fad'a cikin shesshekar gudu. "Bi a hankali mana Amrah. Na sha fad'a miki cewa ki daina irin wannan gudun, wanda har zai sar'ke ki amma bakya ji. Me ya faru ne?" "Umma wata mata ce, gata can sun faka motarsu a k'ofar gidanmu." Dafe baki na yi, na ce, "To fa! Wannan wace mata ce a cikin mota haka? Ko ta yi b'atan hanya ne? To Allah dai Ya sa lafiya." Tun bamu kuma fad'in komai ba sai ga ta ta shigo ciki. Mahaifiyar Annur ce, sanye cikin kaya na al-farma. Fuskarta a sake ta yi sallama, sannan ta k'ariso daga ciki "Marhabun da Hajiya Suhailah. Maraba maraba. Iso mana Hajiya." Da fara'arta kuwa ta iso inda nake, ina k'ok'arin shimfid'a mata tabarma amma ta dakatar da ni, "Ga kujera nan bari na zauna a kai kawai, babu damuwa ai." Ta sakar min murmushi. Zama na yi a k'asa, na gaishe ta ta amsa da sakin fuska. "Maman Amrah kin gane ni kuwa?" Ta fad'a tana kallo na. "K'warai ma kuwa Hajiya. Ba mahaifiyar Annur ba ce?" Jin na ambaci Annur ya sa da sauri Amrah ta iso gare ta, ta duka har k'asa ta gaishe ta. "Lafiya k'alau Amrah. Lallai yarinya ta girma k'warai da ainun. Ya k'arfin jikin naki?" "Alhamdulillah! Jiki ya yi sau'ki sosai Mama. Ina fatan tare kuke da Ya Noor, saboda a ko da yaushe Ummah ce min take wai Ya Noor zai dawo gare ni, kuma gashi har yanzu bai dawo ba." Ta b'ata fuskarta alamun damuwa. Dafa kanta Hajiya Suhailah ta yi, ta murmusa sannan ta ce, "Annur zai dawo insha Allahu nan ba da jimawa ba. Ke dai abin da nake so a gare ki, kawai ki dage da addu'a. Allah ya shawo kan Dady'nsa, ya amince ya dawo gare mu. Ni kaina ina cike da kewar yarona, ina son ya dawo ya ci gaba da rayuwa a gabana." "Mama, har cikin zuciyata nake jin Ya Noor, nake mararin ganinsa. Duk da ban sanshi ba, ba zan iya tuna komai game da shi ba, amma fa ina jin sa har cikin raina, kamar yanda na tabbatar shi ma ina ransa. A yanda nake jin labarinsa a bakin Ummana da kuma Abbana, Ya Noor mutumin kirki ne, wanda ya nuna min zallar soyayya, ya kula da ni, sannan kuma ya bani lokacinsa. Dan Allah Mama, ko a hoto ne ki gwada min shi, yau rana d'aya tal, in ga fuskar wannan bawan Allah, mai tarin halayen kirki. Shekaru kusan hud'u ke nan ina fatan na ganshi ko da a mafarki ne, ko kuma a hoto, amma Allah bai karb'i du'a'ina ba, sai ga ki yau Allah ya kawo ki har inda muke." Murmushi Hajiya Suhailah ta yi, ta ce, "Abin da ya kawo ni ke nan Amrah. Annur ya jima yana rok'ona a kan na zo gidanku, na had'a ku ko da a waya ne ku gaisa, amma ina guje wa maganarsa. Ba dan komai ba, sai dan sanin halin Dady'nsa da na yi. Matuk'ar ya fahimci wani abu to komai zai iya faruwa, saboda shi d'in bai had'a ilimin yaransa da komai ba. Ganin halin damuwar da yake a ko da yaushe, ya sa yau na amince da buk'atarsa, zan kuma yi masa yanda yake so." Ta sake yin wani murmushin had'e da zaro wata leda mai d'an girma daga cikin jakarta. Mik'o ta ta yi ga Amrah, ta ce, "Waya ce wannan ya sa na siya miki, wai yana son ku ringa waya a kai a kai, kuna gaisawa, yana kuma jin halin da kike ciki. A cikinta akwai hotunansa da dama ya turo, idan kin bud'e zaki gani." Tsalle Amrah ta yi cike da murna ta karb'a wayan, a k'irjinta ta d'ora sai faman fara'a take, ta ma kasa furta komai tsabar murna. "To ke baki iya godiya ba ne?" Na fad'a cike da mamakinta. "A'a maman Amrah, bar ta ta yi murnanta. Shi d'in ma ya ji dad'i sosai sanda na amince masa." Ta fad'a had'e da mik'ewa. "Ni zan wuce, sai kuma Allah ya sake dawo da ni. Sannan kuma ina neman wata al-farma a wurinku." Da sauri na ce, "Allah Ya sa zan iya, Hajiya." "Dan Allah ki ringa turo min Amrah tana gaishe ni, lokaci zuwa lokaci. Ina son yarinyar, ko dan soyayyar da Annur yake mata, ita ma kuma take masa. Sannan kuma duk sanda kuke da wata matsala ko kuma damuwa, kar ki ji komai, dan Allah ki same ni da maganar, insha Allahu zan warware miki ita. Amrah dai 'yata ce tamkar Annur, yanda nake jinsa haka ita ma nake jinta a raina, banbancinsu ba wani mai yawa ba ne. Dalilai da dama ne suka hana ni waiwayarku, tun bayan tafiyar Annur. Ciki kuwa har da rayuwar k'unci da na shiga, a lokacin da aka tafi min da yaro. Na ji a raina, bana son ganin duk wani abu da ya dangance shi, saboda tuno min da shi da yake. Baki d'aya komai na shi na kyautar, saboda bana son gani. Shi ya sa na ji ba zan iya zuwa wurinku ba, guje ma tada tabon da ke k'ok'arin warkewa. Hatta da abokanansa na hana su zuwa inda nake, saboda gani nake idan har suka zo, zana ringa masu kallon kamar zan ga Annur a tare da su, bayan kuma ba haka ba ne. Abu na biyu kuma, rabamu da ku da Dady'nsa ya yi, ya mana iyaka da ku ne saboda yaronsa, kuma na san halinsa sarai, matuk'ar ya ga wani abu yana shiga a tsakaninmu, to tabbas komai zai iya yi maku..." Da sauri na dakatar da ita, jin ta yi wannan maganar ya sa na ce, "To kuma Hajiya a haka ne kike so Amrah ta ringa kai miki ziyara?" Murmushi ta yi, "Ko za a tsare Dady'nsu a ce ya gwada Amrah bai santa ba. Bana ji ma ko sunanta ya rik'e har tsawon wannan lokacin. Kuma shi 'din ba mazaunin gida ba ne, yana da manya manyan kamfanoni a Kaduna, da kuma Abuja, wanda suka danganci magani. Kin ga kuwa ina ya ga wani lokacin zama gida, bare har ya kula da masu shiga da kuma masu fita? Har kuma ya iya tantance Amrah, a matsayin yarinyar da Annur ke so, har ya sadaukar da lokacin karatunsa a kanta? Kar ki ji komai Maman Amrah, wannan mai sauk'i ne. Ni dai kam ina son Amrah, kuma na miki al-k'awarin zuwanta inda nake ba zai tab'a saka ku da na sani ba, face shak'uwa da zata k'ara shiga tsakaninta da Annur, wanda nake fatan ya kai su ga yin aure duk sanda suka gama mallakar hankalin kansu." Ajiyar zuciya na sauke, sannan na ce, "To Hajiya, su kuma fa 'yan uwansa? Ina nufin Saddiqa da Islam. A sanina dai su ma d'in basa k'aunar Amrah, saboda suna ganinta d'iyar marasa arzik'i. Kina ganin kamar ba zasu ci zarafinta ba idan tana zuwa gidansu?" Komawa ta yi ta zauna daga kujerar da ta tashi, ta ce, "Maman Amrah ke nan. Ai Saddiqa ta dad'e da yin aure, kusan shekara bakwai ke nan, tana Bauchi a can take aure. Yanzu haka yaranta biyu fa. Islam kuma tana India, a can take karatun medicine. Bata zuwa k'asar nan sai bayan shekara guda guda. Dan haka dan Allah kar ki damu. Ina son Amrah ta shak'u sosai da ni, in bata gatan da ban ba ma yarona Annur ba." Sai a lokacin na samu kwanciyar hankali, na murmusa, "To insha Allahu kuwa Amrah zata ringa zuwa tana gaishe ki duk ranar jumu'a. Sai dai kuma wani hanzari ba gudu ba, Kin san ita d'in yarinya ce mai yawan ciwo, saboda sikilar da ke gare ta Da wuya ta cika sati d'aya da lafiya, ba tare da mun je asibiti ba. Kin ga ke nan, ba ko yaushe ba ne zata samu damar zuwa, saboda yanayin jikin nata." Hajiya Suhailah ta ce, "Haka ne Maman Amrah. Ina mata fatan samun lafiya. Uban-giji ya bata lafiya, ya kawo mata k'arshen wannan wahala ta ta." "Amin." Na fad'a sannan na mik'e, ganin ita ma d'in ta mik'e. Hijabina na ciro daga bisa igiya, na saka. "Amrah ba zaki mata bankwana ba?" Na fad'a ina kallonta. Kunya ta ji da gudunta ta shige dak'i, wai tun daga sanda Hajiya Suhaila ta ambaci aure a tsakaninta da Annur. Har k'ofar gida na raka ta, wata irin b'arkekiyar mota ce aka kawo ta ciki, wadda daka ganta ka san lallai naira ta zauna masu. Sai da ta shiga mota sannan muka sake yin bankwana na dawo gida, zuciyata cike da k'aunar matar, ta matuk'ar burgeni. Yana da wuya a samu matar mai kud'i kamar Alhaji Iqra Al-Hussein, kuma tana son talakawa irinmu. _A yi ha'kuri jiya ba a ji ni ba, mun samu matsalar wuta ne._ Pinky durling💗 *RAZ 2👌🏻* [8/30, 3:32 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 1⃣1⃣ Ko da Mallam ya dawo na shaida masa abin da ya faru, ba kad'an d'in murna ya yi ba. Sosai ya nuna farin cikinsa a fili, dan a zahirin gaskiya, zan iya cewa Mallam ya fi ni damuwar rashin Annur. "Amrah kawo wayar mu ga" ya fad'a yanda zata ji, saboda tun sanda Hajiya Suhailah ta tafi Amrah bata sake fitowa ba, sai yanzu da mallam ya shigo ake kiran sallar magrib. Fitowar kuwa ta yi, hannunta rik'e da kwalin wayar. "Ga ta Abbah.." ta mi'ko masa. Kar'ba ya yi kuwa, nan ya saka sim card d'in da ke cikin pack d'insa, sannan ya saka batirin ya rufe da marfi. Waya ce Nokia asha, kalar ja, mai matuk'ar kyau da d'aukar ido. Kasantuwar Mallam ma yana da waya, ya san kanta, ya sa bai wani sha wahala ba wurin had'a komai yanda ya dace. Ko da ya kunna, hoton Annur ne a saman walfefar wayar, ya yi wani irin k'ayataccen murmushi. Kyakkyawar fuskarsa ta amsa wani irin k'asumba, irin wadda matasa ke tarawa take masu matuk'ar kyau. Gashin kansa kwance yake luf luf, ya tara suma da alamun ya jima bai yi aski ba. Baki d'aya halittarsa ta gama fitowa, tamkar yaron larabawa haka ya koma. Da murna k'warai Mallam ya mi'ke tsaye, donshi har yana k'ok'arin kawo ruwa tsabar farin ciki. "Annur haka ka koma? Allah sarki yarona!" Yana sake kallon hoton. Da murna ni ma na ce, "To ka bani nima na gani mana." Mik'o min wayar ya yi, "Yaro ya zama saurayi son kowa k'in wadda ta rasa. Murjanatu taya ni kallo dan Allah." Kamar wasu kid'mammu haka muka koma, farin ciki kuwa ko d'anmu ne na cikinmu iyakacin wanda zamu yi ke nan. "Umma kawo ni ma na ga Yaa Noor d'in." Amrah ta fad'a, ita kanta da fara'a k'unshe a saman fuskarta. Mik'a mata na yi, ta dube shi da kyau. "Umma ai na san wannan..." ta fad'a cike da mamaki. "Shi ne Yaa Noor d'in?" Cike da mamaki na kalle ta, na ma rasa abin da zan fad'a. "Wallahi Umma da gaske nake na san shi. Yanzu wai baki tab'a kula da shi ba a asibiti idan mun je wani lokacin?" Mallam ne ya iya fad'in, "Anya kuwa Amrah? Ko dai mai kama da shi ne kike gani? Annur fa baya k'asar nan." Sake dubar hoton ta yi, cike da yak'ini ta ce, "Wallahi Abbah na san shi. Kusan sau biyu ko sau uku ina ganinshi a asibiti. Ranar farko ma a wurin ganin likita ne na ganshi, Rana ta biyu kuma cikin keken guragu na ganshi. Na ukun ne dai ba zan iya tunawa ba, amma kam tabbas wannan ne nake gani." Ganin bil-hak'ki take, ya sa na ce, "Wai wace irin magana kike ne Amrah? Kin san shekarar Annur nawa rabonsa da k'asar nan? Kusan fa shekara bakwai ko takwas ke nan. Ba a kama ne a duniya? Wata k'il dai mai kama irin ta shi ce kika gani." Mik'o min wayar ta yi, ta ce, "Umma sake duba shi dai sosai. Na yi mamaki ki ce wai baki ta'ba ganinsa ba. Wallahi Umma duk ganin da nake masa a tare da ke ne. Har ma fa akwai ranar da ya gaishe ki, kin dai manta ne kawai." Kallon mamaki kawai muke binta da shi, saboda yanda muke jin zancen nata kamar a wasa, ga ta ita kuma da gaske take, har tana dagewa rantsuwa. "Umma ashe dama shi ne Ya Noor d'in. To ni dai gaskiya na yi fushi da shi. Ashe yana ganina kuma baya min magana ko? Bayan kuma ya san ina cike da kewarsa, ina son ganinshi sosai." Ta b'ata fuskarta cike da damuwa. Kamo ta na yi na zaunar a kusa da ni, "Amrah! Ki cire tunanin Annur ne kike gani a asibiti. Na fad'a miki cewa ba shi ba ne, Annur baya k'asar nan fa. Kin san ana kamanni a duniya, ta yiu ke kamarsu ce kika gani, bare kuma wannan a hoto ne. Dan haka ki daina wannan tunanin, ta ya Annur da yake mararin ganinki, kuma zai ganki ya share ki? Wannan ba abu ne mai yiuwa ba." Haka na ci gaba da k'ok'arin ganar da ita gaskiya, amma fa sam ta k'ek'ashe ta k'i yarda da maganata. A k'arshe dai ta nunar min da ta yarda, wanda a zahirin gaskiya ba yarda d'in ta yi ba kuma. Haka dare ya yi na ringa juya maganganun Amrah, ban san dalili ba, haka kawai na saka ma kalaman nata alamar tambaya, ta yanda kallo d'aya ta ce ta san shi, kuma har take rantsuwa cewa wai ya tab'a gaishe ni. Washe gari da safe ta yi shirin makaranta. Wata makaranta ce a can k'asan layinmu ta gwamnati take, yanzu haka tana primary 6 ke nan. "Abba baka kira min Yaa Noor d'in ba fa, kuma kai ka ce yau da safe zaka kra min shi kafin na tafi makaranta." Da murmushi Mallam ya ce, "Ai kin ga yanzu fa makaranta zaki je Amra, insha Allahu na miki al-k'awari idan kin dawo zan kira miki shi, tun da akwai kati da kuma lambar wayarsa a nan ciki." "Oya ki yi ki kammala shan kununki ko? K'osan ya ishe ki?" Na tambaye ta. "Ehh, ya ishe ni Umma. Na gode." Bayan ta gama ta zo na saka mata al-barka kamar ko yaushe, na ce, "A yi karatu da kyau 'yata. Ina miki fatan alkhairi. Allah Ya miki al-barka." "Amin Ummana. Bara in tafi." Ta sab'i jakar makarantarta. Bayan ta kusa isa zaure, ta juyo ta d'ago min hannu tana murmushi, wanda wannan d'ago hannun da ta yi, kawai sai na samu kaina da samun rashin kwanciyar hankali. Take gabana ya hau dukan uku-uku. Na d'aga nawa hannun ni ma ina d'aga mata har ta fice. Kallon Mallam da ke shan koko na yi, cikin wata murya mai nunar da fargaba ko kuma shakku, na ce, "Mallam, kawai sai na samu kaina da rashin kwanciyar hankali a kan tafiyar yarinyar nan. Hankalina ya tashi ban san dalili ba." Murmushi ya yi, ya ce, "Murja ke nan. Ban san sai yaushe zaki cire ma ranki irin wannan tunane tunanen marassa ma'ana ba. Ko kin manta addu'ar iyaye ce a kan Amrah? Fita goma zata yi daga gidan nan sai kin saka mata al-barka, sannan kuma ki mata fatan al-khairi. Kin ga kuwa, ai bai kamata ma ki saka wani tunani a ranki ba. Kin san shi shaid'an ta ko wace hanya yana bi dan ganin ya dagula wa mutum lissafi. Ki yi ta'awizi ki kore shaid'an, a duk lokacin da tunani irin wannan ya fad'o miki." Kalaman Mallam suka sa na ji wani sanyi a zuciyata, na kuma samu kwanciyar hankali d'ari bisa d'ari. "Maganarka gaskiya Mallam. Duk wanda al-barkar iyaye ke biye da shi, to tabbas baya tab'ewa. Ko da a ce wani abu zai same shi, matuk'ar ya rik'e adhkar d'insa, sannan iyayensa na saka masa al-barka, ko ma me zai same shi, zai zo masa da sauk'i. To bare kuma Amrah, yarinya 'yar shekara goma, wadda a kullum burinta shi ne ta ga ta faranta mana rai. Ba wai dan Amrah tana tawa ba, amma wallahi zan iya cewa tun da nake a rayuwata, ban tab'a ganin k'aramar yarinya mai kyawawan halaye da d'abi'un kirki kamar ta ba. Dama dukkan hani ga Allah baiwa ne, na gasgata wannan zancen. Gata dai yarinya mara wadatacciyar lafiya, Allah Ya rage ta ta fannin lafiya, amma kuma sai ya wadatar da ita da halaye na gari. Ina mata fatan d'orewa da wannan halaye nata, wanda nake fatan ko bayan babu ita a doron k'asa, zata zama abar koyi da kuma al-fahari ga al-ummah." Daga nan wani irin kuka ya kufce min, wanda na rasa gane ko na me nene. Ajiyar zuciya Mallam ya sauke, "Haka ne Murja. Amrah kam sai dai mu dad'a godiya ga mahalicci. Ga ta da k'walwa, tun daga b'angaren Islama har b'angaren boko d'in. Ta zama yarinyar da duk wani abun da za a yi da ya danganci masu k'ok'ari, to ita ce farkon da za a saka a lissafi. Idan wata gasa ce za a yi da ita a ciki, Musab'aka har ta k'ananan hukumomi ta je, ta wakilci Katsina Local Government, sahun 'yan izib goma. Duka wannan halaye nata sun ginu ne ta dalilinki Murja. Ke ce kika d'ora ta a bisa wannan tafarkin na kirki. Tabbas! Samun uwa ta gari kamar ki sai an tona, ke jajirtacciyar mace ce, abar al-fahari kuma abar kwatance." Du'kar da kaina na yi ina wasa da warwaron hannuna, ina k'ara jin tausayin Amrah a cikin zuciyata. Ba dan komai ba sai dan kasa gafartawa kaina da na yi, saboda na san tabbas mu ne sila, ciwon Amrah tamkar mu ne silarsa. Tun da inda a ce tashin farko mun yi abin da ya dace kafin aure, da duk hakan bata faru ba. Sai dai kuma k'addara ta rigayi fata, kamar yanda Dr. Xarah ta fad'a mana. Da wanann tunanin na mik'e, na tattaro kayana da na Amrah masu datti, zan wanke su. Mallam ya ce, "Na ji fa ta rok'e ki al-farmar kar ki yi wankin nan har sai ta dawo ku yi tare, shi ne kuma kika fiddo zaki yi?" Ajje kayan na yi a k'asa sannan na ce, "Wahalar da yarinyar nan ke yi ce nake ga kaman zata yi yawa Mallam. Ka ga fa Dr. Xarah ta hane mu a kan saka ta aiki da yawa, musamman ma wanda k'asusuwanta zasu yawaita motsawa. Shi ya sa ba zan sake barinta ta yi wanki ba. Girki da shara dai da ba wani wahala ne da su ba, sai in ringa taimaka mata wurin yinsu." "Ehh to, haka ne kuma. Ni bara in tashi in nufi wurin k'wadago. A yi min addu'a." Kallonsa na yi da murmushi na ce, "Allah Ya kare ka da kariyarSa mafificiya. Allah Ya baka ikon ciyar da mu da halal. Fatan al-khairi." "Ameen." Ya fad'a had'e da tafiya. Misalin k'arfe sha biyu na gama komai, har gyare-gyaren gida duka na yi. Muroyoyin yara na ji ana hayaniya sosai, kuma abun na k'ara kusantowa a cikin gidanmu. Saurin mik'ewa na yi jin sun shigo daga zauren gidan, wasu ma har sun iso daga ciki. Ko da suka k'ariso na tambaye su, lafiya? Wata yarinya 'yar za'kal d'insu ce ta yi caraf ta ce, "Amrah Abdallah ce..." muryarta ta sark'e tsabar sauri da take ta fad'a min. Cikin tashin hankali na ce, "Fad'a min me ya faru da Amrata? Me ya samu yarinyata?" "Wani malaminmu ne ya dake ta sume, har yanzu bata farfad'o...." "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" Na furta ban ko jira ta gama maganar ba. _Duk wasu masu cutar sickler, tun daga manya har izuwa k'ananan yara, ina masu fatan samun sauk'i. Allah Ya sauk'ak'a masu, Ya kawo rahamarSa a gare su._ *Ku yi comment da AMEEN, Please👏🏻😢.* Pinky durling💗 *RAZ 2👌🏻* [8/30, 3:32 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 1⃣2⃣ Tafiya nake gudu-gudu, sauri-sauri. Baki d'aya hankalina a tashe yake, ban ma san inda nake dosa ba, sai dai kawai na san biye nake da yaran da suka zo fad'in sak'on. A haka muka isa makarantar, kai tsaye muka nufi ofishin head master tare da yaran. Amrata na gani kwance tamkar bata numfashi, malamai kusan guda biyar zagaye da ita, wani na tofa mata addu'o'i wasu kuma tagumi suka yi cike da tausayinta. "Amrah!" Na fad'a a firgice. "Ku fad'a min dan Allah me ya faru da 'Yata? Me aka mata?" Na jawo ta na rungume tsam a jikina. "Wallahi idan har yarinyata ta mutu ba zan tab'a yafe wa hukumar makarantar nan ba. Tun lokacin da za a saka ta sai da muka zo nan tare da mahaifinta, ya maku bayanin lalurinta, gashi a k'arshe kun kasa kare min yarinya. Wallahi matuk'ar ta mutu sai na yi shari'a da hukumar makarantar, in ya so sai ku fitar da ko ma wane malami ne ya mata wannan dukan." Kuka sosai nake, ina sake dubar jikinta da aka farfasa da bulala, har a lokacin jini bai daina kwarara ba. Wannan yarinyar 'yar zak'al ce ta ce, "Kuma wallahi Mama ba fa ita ce ta yi laifin ba. Amrah babu ruwanta da kowa, bata fitina, ko fad'a ta ga ana yi a cikin ajinmu ma fita take. Sai da ta rantse ma Mallam Mu'ammar cewa ba ita ce ya aika ba, amma ya ce wai ita ya aika ta d'auko masa red pen d'insa a staff room, gashi kuma bai ga sabon littafinsa ba, wai ita ce ta sace. Duka 'yan ajin sai da muka bata shaida, amma bai yarda ba, sai da ya mata wannan wawan dukan." Kai kawai na gya'da, hankalina a tashe na sab'e ta had'e da mik'ewa. Ban san ma ya zan yi ba, kasantuwar ban fito da ko sisi ba tsabar tashin hankali. Wani Malami wanda na tarar yana mata addu'a ne ya ce, "Mu je na kai ku asibiti a mashin." Ban musa masa ba, dan bani da wani zab'i da ya wuce na bi sa d'in. Head master'n ne ya zaro dubu d'aya daga aljihunsa, "Mallam Hafeez ga wannan, ko da za a buk'aci kud'i." Ya juyo gare ni, "Dan Allah Hajiya a yi hak'uri, an yi kuskure wanda k'addara ce kuma ta rigayi fata. Insha Allahu hakan ba zata sake faruwa ba. Fatanmu dai yanzu ta farfad'o, sannan duk maganar da za a yi a yi." Ko kallonsa ban yi ba kawai na fice, da sauri malamin da aka kira da Mallam Hafeez ya biyo bayana. Bakin mashin d'insa ya isa, ya fiddo sannan na hau ina rungume da Amrah. Tambayata ya yi asibitin da muke kaita na fad"a masa, hakan ya sa kai tsaye muka doshi can d'in. Muna isa risafshan da sauri na k'arisa inda medical recoarder yake, tsabar yawan zuwa asibiti har ma na hardace lambar katinta, babu b'ata lokaci ya fiddo fayil d'inta. Ganin tana unconcious ya sa ko tsayawa bin layi bamu yi ba, kai tsaye aka shigar da fayil d'in nata muka shiga wurin likita. Dr. Rabi'atu ce yau muka tarar, ganinmu ya sa ta zare glasses d'inta cike da tausayi ta ce, "Amrah jikin dai?" Ta karb'e ta daga hannuna. "Ehh..." kawai na fad'a ina son ci gaba da magana amma tashin hankali bai bar ni ba, sai faman kuka nake tamkar yau ne ta fara yin ciwon. Da k'yar na iya jawo magana daga k'asan mak'oshina, na ce, "Dr. Tun da yarinyar nan take ciwo bata tab'a irin wannan ba. Duk irin sumar da zata yi bata wuce minti biyar ko goma ta farfad'o. Amma ki ga wannan, tun d'azu take a haka, ga jikinta ya yi zafi rau kamar garwashi." Kuka ya sake cin k'arfina. Ajiyar zuciya Dr. Rabiatu ta sauke, "To yi hak'uri Maman Amrah, daina kukan mana. Insha Allahu zata samu sau'ki. Amma me aka mata ne har haka?" "K'awayenta ne suka zo har gida suka shaida min, wai wani malami ne ya dake ta." Na bata amsa ina mai k'ok'arin had'iyar sabon hawayen da ya fito min. "Subhanallahi! Dama kuwa akwai irin wannan malaman, wanda basu da tausayi ko kad'an. Banda abinshi, ina abun duka ga wannan 'yar halittar? Idan ma dukan ne, ai sai ya san kalar wanda zai mata. Amma ki ga fa, har yanzu jini bai tsaya ba." Ta hau dudduba ta. "Ina ga kaman dole sai ku kwanta fa, ko da kwana d'aya ne ta yi sannan. Tana da bu'katar kula sosai a nan kafin ku koma gida." Mik'o min ita ta yi, sannan ta rubuta wata allura ta bani, "Ki karb'o wannan allurar yanzu a famasi, sai na mata ita kafin komai." Mik'ewa na yi a hanzarce, na nufi d'akin magani da takardar. Su kansu sun san ni, sun san cewa a kyauta muke karb'ar duk wani maganinta ko kuma allura. Bani allurar suka yi da sauri na koma wurinta. Bayan ta karb'a, ta had'a ta sannan ta sa na kwantar da Amrah a bisa gadon da take duba marasa lafiya. Allurar ta mata, wanda sai a lokacin na d'an samu kwanciyar hankali, ganin yanda ta d'an zabura a lokacin da allurar ta shiga cikin fatarta. Bayan ta gama ta jefa allurar a cikin dustbin, sannan ta dawo mazauninta. "Ki je nurses station ki kira min duk Sister d'in da kika had'u da ita." Ta ce da ni. "Daga nan ki kira min patient na gaba." Fitar kuwa na yi, bayan na turo mata nurse ne ta umurce ta da a kaimu d'akin irin na mutum d'aya d'in nan (amenity) sannan ta dawo ta kar'bi sauran magungunan da ta rubuta ta karb'o a pharmacy, idan ta farfad'o sai a bata su. Ina fita na ci karo da Mallam Hafeez, ya tambaye ni halin da ake ciki na shaida masa, sannan na bi bayan nurse d'in. Bai tsaya ba shi ma d"in binmu ya yi a baya, kwantar da ita ta yi sannan ta tafi ta bar mu a wurin ni da Mallam Hafeez. "Alfarma guda tal nake nema a wurinka Mallam Hafeez." Na furta ina mai dubansa. "To Maman Amrah." Ya fad'a had'e da matsowa bakin gadon. "Dan Allah wurin k'wadagon mahaifinta zan kwatanta maka, ka taimaka ka shaida masa halin da muke ciki." Na kwatanta masa inda Mallam yake gyaran babur a k'ark"ashin wani bayerabe. Dubu d'ayar da Head mastet ya bashi ce ya zaro ya bani, sanann ya tafi. Bayan tafiyar Mallam Hafeez ba da jimawa sosai ba Amrah ta tashi, hawaye duk ya bushe a kumatunta. Da hanzari na isa gare ta, bin ta nake da kallo har sanda na k'arisa dai-dai gadon da take kwance. Ganina da ta yi cikin yanayin damuwa da kuma tausayinta ya sa ta sakar min murmushi, "Ummah..." ta k'o'karta fad'i annuri bai kau daga fuskarta ba. Duk da na san cewa 'karfin hali ne irin na Amrah, a rayuwarta ko kad'an bata so ta ganmu cikin damuwa, ba wai mu iyayenta kad'ai ba, kowa ma. A haka ni ma na sakar mata murmushin wanda iyakarsa bisa fuskaka kawai ina kallonta. "Sannu Amrah." Na fad'a cike da tausayi. "Yauwa...Ummah, k'ashin bayana ciwo kamar zai tsage." Ta fad'a tana k'ok'arin kai d'ayan hannun da ba a lik'a mata drip ba a bayan. "Dama dole zai miki ciwo ai. Ki kwantar da hankalinki, zan kira Nurse yanzu zata baki kulawa sosai. Insha Allahu yanzu zai daina yi miki ciwon." Na kama hanyar nurses station. "Sister ta farka...ina nufin Amrah Abdallah, mai sickle cell." Da hanzari ta tashi tsaye, wani kwando ne wanda already ta had'a medications d'in Amrah baki d"aya. Na yi gaba ta biyo ni a baya. "Ki samo mata ruwa tukuna, wanda zata sha maganin da shi." "To Sister." Na fad'a ha'de da nufar wajen asibitin. Da kud'in da Mallam Hafeez ya bani na siyo mata ruwa da lemo, sai kuma biskit. Bayan na iso, zaune na same ta, Sister kuma tana b'ab'ballo mata magnungunanta, tana d'orawa a wata container wacce suke saka magungunansu a ciki. "Umma yanzu ya bar wurin nan..." ta fad'a cike da mamaki tana nuna k'ofa. "Umma baki had'u da shi ba?" Bayan na k'ariso ciki na tambaye ta, "Wa ke nan?" Had'e da d'ora robar ruwan sona a bisa teburin ajiye-ajiye. "Umma, Ya Noor mana." Ta furta cike da yak'ini. Gyad'a kai kawai na yi, dan a tunanina ko zafin ciwo ne kawai ya sa ta fad'in hakan. "Umma wallahi da gaske nake. Sister dan Allah ba yanzu wani gurgu ya bar nan ba?" Kai sister'n ta gyad'a alamar ehh. "Na san ke ma kun had'u a dai-dai shigowarki sai dai ko baki ga fuskarsa ba ne. Amma wallahi Umma shi ne nake gani. Na fad'a maku ke da Abba kun k'i yarda. In dai wannan wanda kuka nuna min a hoto shi ne Annur, to tabbas shi ne yake kai da kawowa a cikin asibitin nan." Kai na dafe cike da mamaki, tabbas na ha'du da wani a cikin keken guragu, sai dai kuma ban tsaya na kalli fuskarsa ba bare na tabbatar da gaske ne ko akasin haka. Zama na yi ba tare da na sake furta komai ba, sai binta da kallo kawai da nake tana dafe da bayanta, amma hakan bai hana ta k'ok'arin tabbatar min da gaskiyarta ba. "Maman Amrah, sai a kula sosai da magungunan nan. Sannan kuma a kula kar ta yawaita motsawa har sai sanda allurar nan ta sake ta sosai. Ko fitsari zata yi gwara ki fita waje ki siyo mata fo, dan yawaita motsawar kanshi zai iya lalata mata treatment. Sannan kuma sai kin yawaita tab'a jikinta, idan kika ji zazza'bin yana yawiata sauko mata sai ki kirani, Ina jin dole za a mata awon jini dan tabbatar da ya k'one ko bai k'one ba? Sannan a san madosa." "To insha Allahu zan kula Sister. Na gode Allah Ya saka da alkhairi." "Ameen maman Amrah. Allah Ya bata lafiya." Daga nan ta fita ta bar mu. Tana fita sai ga Mallam Hafeez a gaba, sai Mallam biye da shi, hankalinshi a tashe. "Amrah 'yata me ya same ki?" Ya furta cike da damuwa, yana k'ok'arin isowa bakin gadon da take kwance. "Sannu kin ji? Ashe ciwo ya tashi, Allah Ya kyauta ya tsare gaba." "Ameen Ya Allahu." Mallam Hafeez ya furta. Sai a lokacin ma na tuna da ba a mata treatment na raunin da aka mata wurin bulala ba. Da hanzari na ce, "Mallam ina zuwa." Na nufi wurin Sister. Bayan na fad'a mata dalilin zuwana ta ce, "Ehh ina sane da shi ai, small injury ne ba abun a damu sosai ba. Gwara a bar mata shi a bud'e ya sha iska, Dan kar a je a tab'a k'ila k'ashin wurin bashi da wani k'wari sosai. Wurin gyaran gira a rasa ido." Na gamsu da maganarta sosai, hakan ya sa kawai na mata godiya had'e da tafiya. _Yawan zazzab'i mai zafi wanda baya sauka, yana d'aya daga cikin alamomin sickler. Lura da kyau, mu zama masu kula da ciwukan da yaranmu ke yi, kar mu zama masu sake, har ciwo ya fara yi masu yawa. Allah Ya bada lafiya._ Pinky durling💗 *RAZ 2👌🏻* [8/30, 3:33 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 1⃣3⃣ Washe gari da sassafe sai ga Malaman makarantarsu sun zo, su kusan ashirin ko ma fin haka. Har d'akin ma bai iya d'auke yawansu ba. A lokacin da suka zo Mallam baya nan, ya zo ya kawo mana abinci, ya wuce wurin aikinsa. Har k'asa na du'ka muka gaisa, sannan na d'an bubbuga Amrah ta tashi. Head master'nsu ne ya 'kariso dai-dai inda take, "Sannu Amratu. Ya k'arfin jikin naki?" Da fara'a k'unshe a fuskarta ta ce, "Jiki da sau'ki sosai Mallam. Na gode." Da haka malaman sukaita mata ya jiki, a k'arshe Mallam Mu'ammar cike da kunya ya dafe k'eyarsa, ya ce, "Insha Allahu hakan ba zata sake faruwa ba. A yi hak'uri." Ya juyo gare ni, "Ban tsammanin abun zai kai har haka ba, da tun farko ban dake ta ba. Insha Allahu ba zan kuma maimaitawa ba. Zan zama mutum mai tausayi, ba wai gare ta kawai ba, ga baki d'aya d'alibaina." Ya juya ga sauran Malaman ya ce, "Dan Allah ina mai neman afuwarku, daga yanzu duk wani d'alibi wanda za a kawo mai sickler, mu ringa kula da shi, mu san ta hanyar da zamu masa hukunci. Sai mun kula sosai, mun basu kulawa tamkar 'ya'yanmu ko kuma k'annenmu na jini. Ita rayuwar nan baka san wanda zai maka rana ba, sanann kuma kana naka Allah Na naSa." Head master ya yi gyaran murya ya ce, "Haka ne Mallam Mu'ammar. Na ji da'di k'warai da ka gane hakan, har kake bada taka shawarar. Allah Ya tsayar nan, ita kuma Allah Ya bata lafiya." "Ameen." Duka Malaman suka fad'a a tare. Ku'di Head master ya zaro daga aljihunsa ya d'ora bisa gadon Amrah, "Ga wannan a sai miki lemo. Allah Ya sauwak'a ko?" Godiya na masa sannan suka fita, suka bar d'akin baki d'ayansu. Bayan sun tafi na duba kud'in, dubu goma ne cif, hakan ba kad'an d'in dad'i ya min ba, saboda dama babu kud'in, abincin da Mallam ya siyo mana da safe ma da k'yar ya had'a ku'din ya siyo. Kwananmu biyu aka bata sallama muka koma gida, ranar da muka koma sai ga Hajiya Suhaila ta zo, wai Annur ne ya fad'a mata Amrarsa bata jin da'di, da yake ya kira ta wayar Amrah'n Mallam ya d'auka yake shaida masa bata da lafiya, kuma baya asibiti a lokacin bare su yi waya. Ta kawo ma Amrah sha tara ta arzik'i, a 'karshe ta mana fatan alkhairi sanann ta tafi. Da yamma Mallam ya kira ma Amrah Annur. Sun jima suna waya, har take masa ta'din ganinsan da take yawan yi a Turai Hospital, amma ya shaida mata cewa ba shi ba ne, saboda shi tun da ya bar Nigeria bai sake dawowa ba. Wata k'ila dai mai kama da shi ne kawai take gani. Rayuwa ta ci gaba da tafiya a haka, yau da lafiya gobe babu lafiya, a haka dai take rayuwarta cike da wahala. Talauci kuma sosai muka rage shi, saboda babu abin da Hajiya Suhaila bata bamu, tun daga kan kayan abinci har sutura yi mana take, Amrah ma kuma ba laifi tana zuwa gidanta, abin dai sai sam barka. A lokacin da Amrah ta yi JSS ne, take da shekara goma sha uku da watanni. Ranar da suka gama zana jarabawarsu, Annur yake mata albishir da cewa mahaifinsa ya barshi ya dawo Nigeria ya ci gaba da aikinsa, saboda ya da'de da zama Architecture babba, wanda yake da degree mataki na uku (ph. D) duk a 'bangaren zane-zane. Sosai Amrah ta yi murna, dan zan iya cewa ko Hajiya Suhaila da ta haife sa, bata kai Amrah jin dad'i ba. Ranar da suka yi waya cewa zai dawo gobe, kasa bacci Amrah ta yi, sai faman juye-juye take, ta ma rasa me ya kamata ta yi saboda murna. Washe gari da sassafe ta fito tsakar gida ta hau shara, jin motsinta ya sa na fito a hanzarce na ce, "Ya da shara tun da duku-dukun safiya, ba zaki yi shirin makaranta ba?" Fuska a yamutse ta ce, "Umma yau fa ba zan je ba. Kin manta Hammana zai dawo?" Murmushi na yi na ce, "Ya za a yi na manta da dawowar Annur? Ai ban ga zaman me zaki yi ba idan baki je ba? Ga ki kuma ke ce shugabar aji." "Umma ai jiya Momy ta kira ni, wai yau da safe na je can mu yi shirye shiryen tarbarsa. Shi ya sa ma na tashi da wuri dan na kammala komai cikin lokaci." "To ai shi ke nan. Amma ba kya gudun abin da Islam zata miki? Kin san fa ita ma yau tana iya k'in zuwa aiki saboda shi." Tab'e baki Amrah ta yi ta ce, "Duk abin da ta min ai sai in bata ha'kuri. Cike nake da murna yau bana jin masifarta da wulak'ancinta zasu yi tasiri a gare ni, har su hana ni tarbar Ya Noor." Ajiyar zuciya na sauke, "To ai shi ke nan. Amma sai kin daure, kin kai zuciyarki nesa." "Insha Allahu kuwa Ummah. Ai kin san ni da wuya mutum ya b'ata min rai. Ina binsa da yanda yake so, sai dai ma a k'arshe shi d'in zai ji kunya." "Na tabbatar da hakan kuwa 'yata. Allah Ya miki albarka ya sa ki d'ore da wannan kyawawan halayen naki. Wai har yanzu ba a saka ranar walimar saukar taku ba?" "Basu saka ba Umma. Amma dai na san very soon za a yi ta. Shi ya sa ma suka ce kowa ya zama cikin shiri. Har ma na gama tsara ma d'alibaina diramar (darama) da zasu yi ta larabci." Murmushi na yi na ce, "Ke d'in nan ce da d'alibai? Lallai ma." "Umma kar dai ki ce baki san cewa ina da d'alibai ba? Tun bayan da muka yi sauka da tilawa aka raba mana azuzuwa. Sauran "yan ajinmu ma aka fitar masu da aji...?" "To bare kuma ke da kike Amira (Head girl)." Na k'arisa mata had'e da murmusawa. "Ni dai ban fad'a ba Umma." Ta furta tana murmushi. "Ai na san can kika dosa." Ci gaba da sharar ta yi har sanda ta gama. Zata yi wanke wanke na dakatar da ita, "Je ki shirya kawai ki bar min wannna zan yi. Dan na ga a matse kike sosai." "A'a Umma. Wallahi ki bari zan yi kawai. Wanke-wanken duka nawa yake?" Ta ci gaba da ha'da ruwan kumfa. "Sanin bashi da yawan ne ai ya sa na ce miki ki bari na yi. Kullum fa ke ke yi, yau rana d"aya dan baki yi ba ai ba damuwa." Da 'kyar na samu ta bar wanke wanken na ci gaba. Ita kuwa ta nufi wanka. K'arfe goma saura wayarta ta hau ruri, ganin Momy rubuce ya sa ta hanzarta d'auka, "Assalamu alaikum." Ta furta had"e da matse wayar da wuyanta, tana shafa kwalli. "Ehh Momy saura k'iris na gama. Gani nan zuwa yanzu insha Allahu." Ta d'an yi shiru daga nan, "Da azahar? Ahh lallai to bara na hanzarta. Ashe ma isowar wuri zasu yi." Ta tsinke wayar had'e da mik'ewa. "Umma bara na tafi. Da azahar wai jirginsu zai sauka. So nake Ya Noor ya fara cin girkina idan ya iso. Ni da kaina zan masa abin da yake so. Dama ya min text na favorite d'insa (abincin da ya fi so)" "To shi ke nan Amrah. Allah Ya miki albarka ya sa a fita lafiya a dawo lafiya." "Amin, Ummana." Ta furta had'e da fita tana murmushi. Ko da ta isa ta samu Hajiya Suhaila sai ujila take, bata can bata can ana ta aikin tarbar bak'i. Ashe wai har da Nadrah babbar yayarsu da yake gidanta zasu zo. Saddiqa ma tana kan hanya ita da yaranta, Islam kuma tana da theatre k'arfe sha biyu, hakan ya sa ta shirya ta bar gidan da wuri. Haka sukaita aiki har sha biyu da rabi sannan Hajiya Suhaila ta ce ta bar sauran aikin ga mai aikinta Safina, zasu tafi Airpot ne dan ta san suna daf da isowa. Wani wankan ta sake yi, sannan ta saka wata doguwar rigarta kalar baby pink, wadda aka k'awata da adon duwatsu hot pink. Gyalen rigar ta yafe wanda shi ma kalarsa hot pink ce. Asalin rigar ma Hajiya Suhaila ce ta siyo mata ita daga Umra da ta je. 'Karfe d'aya da rabi ta masu a Airpot d'in Umaru musa Yaradua. Suna isa suka tarar da Saddiqa da yaranta uku sun isa, saboda dama a can suka yanke sahawarar had'uwa kawai. A yanda Amrah ke bani labari; sun yi zama kamar na kusan mintina arba'in kafin k'arar jirgi ta dake dodon kunnuwansu. Har da hawayen murna ta yi, a dai-dai lokacin da jirgin ya sauko k'asa. Babban farin cikinta, shi ne yau zata ga farin cikin rayuwarta. Zata ga mutum ma fi soyuwa a zuciyarta, wanda ta ta'allak'a rayuwarta da shi. Bata san shi ba, bata tab'a ganinshi ba, tun bayan sanda ta yi wayo, amma a zuciyarta tamkar sun saba ne, wata irin shak'uwa take jin sun yi, a tsawon lokutan da suka d'auka suna waya. "Mommy sun fara fitowa." Muryar Saddiqa ce ta dawo da Amrah daga birnin tunanin da ta lula. Murmushin yak'e ta yi, ganin ta kalli Saddiqa amma ta wurga mata wani matsiyacin kallo. Bin bayansu ta yi, zuciyarta cike da tunane tunane, na yanda zata ga Hammanta Noor. Amrah ba yarinya ba ce mai hanzari, komai nata cikin sanyi take yinsa, hakan ya sa suka mata nisa. Da sauri Salmah ta dawo ta kama mata hannu, "Aunty ki yi sauri mana. Kin ga har an miki nisa." Murmushi ta k'irk'iro ha'de da 'kara saurin tafiyarta. A lokacin da suka isa iyaka, wato daga inda ba za a barsu wucewa ba, har sai sanda matafiyan suka fito da kansu. Dakatawa suka yi, Salmah na k'ok'arin jan Amrah da hira, amma Mamanta Saddiqa ta daka mata tsawa, wanda dolenta ta yi shiru. Tun daga nesa ta hangoshi, bayanshi goye da bak'ar jika, sai kuma wani babban trolly da ya jawo da hannunsa. Biye da shi Nadrah ce, sai yaranta twins 'yan mata, wanda a girme sun girmi Amrah. Kallonsa take tun daga nesa, bata gama gasgata tunaninta ba har sai sanda ya k'ariso inda suke. Fuskarsa yalwace take da annuri, idonshi k'yam a kanta. "Shi ne..." ta furta a razane, tana nuna shi da yatsa. "Ko shekaranjiya ba na ganka ba a asibiti? Yaushe ka warke? Yaushe ka daina hawan keken guragu?" Har a lokacin bata ajje hannunta daga nuna san da take ba. _Daga lokacin da yaro mai sickler ya haura ma shekara uku, za a iya ganin idanuwansa suna canzawa, suna rikid'ewa daga ainahin yanda suke. Wasu kuma hak'oransu jajaye ne. Duk iya k'ok'arin na brushing d'in da ake masu, ba zasu tab'a zama farare ba. Wannan duk cikin alamomin sickler ne. Da zarar kuka ga haka, hanzarta kai yaronku asibiti domin a masa awon genotype. Allah Ya kare mu da ahalinmu baki d'aya._ Pinky durling💗 *RAZ 2👌🏻* [8/30, 3:34 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 1⃣4⃣ _Sakon gaisuwa bad'e da jinjina ga *ANEESA ABUBAKAR RIMI (ANEELURV)* You are indeed a nice person to me, and to everyone. May Allah continue to bless you. Allah Ya barki da Oga._ *** Ba wai Annur kad'ai ba, ita kanta Hajia Suhaila sai da ta yi mamaki, mamakin kalaman da ta ji suna fitowa daga bakin Amrah. Kamar butum butumi Annur ya koma, bai d'auke kallonshi daga gare ta ba, bai daina mata kallon yaushe rabo ba, sai dai tabbas yana matu'kar al'ajabin furucin da ke fita a tsakanin lab'banta. "Baki da hankali ne da zaki danganta Annur da wani gurgu? To ta Allah ba taki ba! Bakinki ya sari d'anyen kashi. Insha Allahu har abada Annur ba zai ta'ba zama gurgu ba. Sai dai ki ga gurgunta a ta b'arahinki." Hajiya Suhaila ce ta dakatar da ita da fad'in, "Ya isa haka, Saddiqa! Wai sai yaushe ne zaki fara sanin darajar d'an Adam? Sai yaushe ne zaki san irin darajar da Amrah take da shi a zuciyata? Idan ma baki sani ba to yau ki sani, banbancinki da Amrah a zuciyata ba wani mai yawa ba ne. Ina nata son da nake wa kaina irinsa. Saboda haka, matuk'ar kina son farin cikina, to ya zama dole ki so abin da nake so. Ki so Amrah tamkar yanda zaki so Islam. Saboda wata rana ita ma ina sa ran zata dawo cikin zuri'armu." Lokaci d'aya ya yi gaggawar sauke idanuwansa daga nata, ya fara k'ok'arin kawar da tunanin da yake. "Barkanku da isowa." Hajiya Subaila ta furta, had'e da rungumar jikokinta 'yan biyu, masu kama iri d'aya. Nadrah ce ta kalli Amrah had'e da sakar mata kakkausan murmushi ta ce, "I guess, ke ce Amrah, right?" Murmushin da Amrah ta yi ne ya tabbatar mata da hasashenta. "Ai ko ba a fad'a min ba dama na san ke ce. Saboda yanda na karanci fuskarki da ta Noor a lokacin da muka k'ariso. Mu isa gida ko?" Murmushi kawai Amrah ke yi ba tare da ta furta komai ba. Duk irin mararin da take na ganin Hammanta, amma ta kasa yi masa magana. Kunyarsa take jin tana ratsa ko wace gab'a ta jikinta. Kasantuwar dama da prado suka zo, hakan ya sa ta kwashe su su duka, in banda Saddiqa da suka tafi cikin motarsu ita da yaranta, banda Salmah da ta nace sai inda Amrah take zata bi. Sai kusan la'asar sannan suka iso, take gida ya kaure da murna, yau dai family'n Iqra Al-Hussein sun yi had'uwar da suka jima basu yi irinta ba. Sun samu har Islam ma ta dawo, a yamutse ta fito babban falon da aka k'awata da wasu manyan takardu da aka rubuta *WELCOME BACK YAYA NOOR!* Wanda ba wata ta yi wannan aikin ba face Amrah, dama ta riga ta gama komai, sanda zasu fita ta bar ma Safina cewa ta bi ko ina ta lilli'ka mata takardun. Haka aka yi zaman cin abinci, murna fal a fuskokinsu, sab'anin Islam da tun da ta ma Amrah kallo d'aya bata sake had'a ido da ita ba, tsabar tsananta da ta yi. Haka yammacin ranar ta kasancewa wannan ahali, farin ciki sosai da nisha'di, wanda zan iya cewa Annur da Amrah sun fi kowa jin dad'in wannan yanayi. Daf da magrib Amrah ta d'auko jikar kayanta cewa zata tafi gida, saboda wata tarbiyya da ta samu, a duk inda take, matu'kar magrib ta kunno kai to hankalinta na karkatowa zuwa gida. "Momy ni zan tafi. Na gode 'kwarai." Ta furta a tsanake. Cikin magabarta dalla-dalla kamar 'yar koyo. Salma ta taso da sauri ta rungume ta, "Aunty dama ba a nan zaki kwana ba? Dan Allah mana ki kwana, wallahi zan miki fira mai dad'i." Murmushi Amrah ta mata, "Na baro Ummana da kewana ne. Insha Allahu gobe da na dawo daga School zan zo." Ta dafa kanta. D'aya daga cikin 'yan biyun Nadrah mai suna Janan ce ta taso ita ma da murmushi a saman fuskarta ta ce, "Aikam dai Amrah da kin tsaya kin kwana. Zan rakaki yanzu ki tambayo Maman taki pls. I need you by my side. Kina burge ni saboda son da Uncle Noor yake miki." Ajiyar zuciya ta sauke, tana k'ok'arin yin magana ne ta ji 'yar uwarta mai suna Hanan ta ce, "Abeg let her go, Janan. Ke shisshihinki ke had'a ni da ke." "Ehh d'in miye ruwanki?" "Ya isa haka ni dai. Ku barta ta tafi yamma na mata. Bata da wadatacciyar lafiya ne kuma ga sanyi sanyin yamma na saukowa. Amrah sannu da k'ok'ari, mun gode k'warai. Ki gaishe da Umman taki." "To zata ji k'warai Momy. Sai da safe." Mik'ewa Annur ya yi ya ce, "Momy bara na raka ta, daga nan ma sai mu gaisa da Umma." Kallonsa Amrah ta yi da murmushi, mai cike da soyayya ta ce, "Allah Yaa Noor da ma ka barshi, ka zauna ka huce gajiya kawai. Gobe ba sai ka je ba?" "An k'i a bari d'in. Wato ke kad'ai zaki ganta ni ba zan ganta ba ko? Sai na je." Ya bi bayanta. Su Islam tamkar zasu fashe tsabar takaici, su dai sun tsani Amrah babu dalili. Ko kuwa dai kasantuwarta 'yar talakawa ce ya sa suka tsane ta? Allah masani. Dai-dai ana kiran magrib suka iso, a lokacin ina d'ibarwa mallam ruwan alwala, wanda dawowarsa gidan ke nan. Baki sake, fuska d'auke da murmushi nake kallonshi, kallon yanda ya koma a zahirinsa, ya zama cikakken mutum, tamkar wanda ba d'an shekara ashirin da biyar ba. Shi d'in ma murmushi k'unshe a saman fuskrsa ya k'ariso ciki, har k'asa ya du'ka ya gaishe ni. "Sannu Umma. Ina wuni?" "Lafiya k'alau Annur. An dawo lafiya ko?" Na fa'da har a lokacin fuskata bata daina murmushi ba. "Alhamdulillahi Umma. Mun same ku lafiya" Ya furta had'e da tashi ya isa inda mallam yake zaune, shi kad'ai sai kallon Annur yake yana murmushi. "Lafiya lau fa." Na bashi amsa. Gaisawa suka yi da Mallam sannan ya mik'e. "Bara na koma. A gajiye nake lis wallahi. Kuma akwai wani aiki da nake son yi a cikin daren nan." A tare ni da Mallam muka furta "To Allah Ya hutar da gajiya." Har k'ofar gida Amrah ta raka shi sannan ta dawo. A ranar da suka cike kwana biyu da zuwa ne sai ga Annur da Janan sai kuma Salmah sun zo a cikin mota. Jaye suke da wani babban akwati, wanda na rasa gane ko na menene. Janan ce ta furta "Wannan tsarabar Amrah ce, daga Uncle Noor." "To fa!" Na furta had'e da mayar da kallona ga Annur. Tun ban fad'i komai ba ya gaggauta fita daga gidan. "Wai duk Amrah kad'ai? Lallai a gaishe da Annur. Allah ya saka masa da alkhairi." "Ameen Umma." Janan ta furta had'e da mik'ewa. "Ban ga Aunty ba." Salmah ta fad'a tana wawware ido. "Wai Amrah? Bata dawo daga makaranta ba." Na bata amsa. "To idan ta zo a gaishe ta please." Har k'ofar gida na raka su, na ma Annur godiya sosai sannan na dawo gida. Bayan azahar ta dawo, a lokacin muka bud'e kayan muka hau duddubawa. Kaya ne masu kyau, k'ananan kaya da kuma material irin na manyan yara. Takalma da jaka saiti biyu. A take na sa ta ta kira Annur ta masa f Godiya, na kuma shaida mata cewa ta fad'a masa, zamu zo har gida mu yi godiya. Tun bayan dawowar Annur, rayuwa mai cike da k'aunar juna ta 'kara bun'kasa a zuciyoyinsu. Soyayya suke mai cike da tsafta, wadda su kansu basu san cewa soyayya ba ce, sai dai kuma duk wanda ke tare da su, dole zai fahimci hakan. Gashi dai k'aramin yaro, mai k'ananan shekaru, amma ya zama d'aya daga cikin manya manyan masu zane, wanda sunansu ya kewaye k'asar Nigeria. Yau ta kasance ranar lahadi, wadda a yau ne za a gudanar da walimar saukar Al_Qu'ani mai girma ga su Amrah. Wanda suka samu nasarar haddace wa baki d'aya. Su biyar ne kuma kacal za a yi ma wa. Wannan walimar babba ce sosai, wadda tana d'aya daga cikin walimu manya da za a gudanar a jihar Katsina. Akwai manya manyan ba'ki wanda zasu halarci wannan walima, ciki kuwa har da gwamnan jihar, da wasu daga cikin masu fad'a a ji dake jihar. Bakin Amrah bud'e yake, saboda kusan in ce ta kai shekara d'aya tana shirin tarar walimar, ta jima tana shirye shiryen yanda walimar zata kasnace. Cikin jerin mutanen, Annur ne zaune cikin wata farar shadda, d'inkin babbar riga wanda ya amsa sunansa. Bakinsa a bud'e yake, yana mai bibiyar duk wani motsi na Amrah, har a lokacin da aka fara gabatar da walimar. _Kar mu yawaita dukan yaranmu masu sickler, saboda ita d'in cuta ce wacce take bin duk wasu k'asusuwa na jiki, take rage masu armashi, take neman dagula al'amurransu. Matuk'ar muka daki yaronmu, k'ashinsa zai iya samun matsala, wanda a k'arshe za a dawo ana regretting. Mu kula da kyau, sai mu san hanyar da zamu bi wurin horonsu._ A yi hakuri da ni, an mana ruwan sama ne wanda ya guyara mana wutarmu, abin dai sai hamdala. Pinky durling💗 *RAZ 2* [8/30, 3:34 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 1⃣5⃣ Bayan gabatarwa da aka saurara daga shugaban makaranta, sai sauraran karatun littafi mai tsarki daga d'alibai. Amrah ce ta k'arshe, inda ta karanto wasiyyoyi da Allah mad'aukakin sarki Ya lissafo a cikin suratul an-am. K'ira'a ce mai matuk'ar da'di, tamkar d"iyar larabawa haka take rero karatunta. Bayan ta gama ne ta koma mazauninta, inda aka tanadar domin zaman mutum biyar d'in da suka hardace littafi mai tsarki. Daga nan sai da wasu d'alibai suka fito suka rero 'yan wa'kok'i irin na larabawan nan masu matuk'ar dad'i, sannan ne aka kira Amrah, in da zata kira d'alibanta domin gabatar sa dirmar da ta shirya masu. Babban abin burgewa a cikin wannan dirama shi ne; yanda yaran suke k'ananan yara, duk cikinsu babu wacce zata haura ma shekara bakwai a duniya. Bayan sun kammala da harshen larabci ne, Amrah ta kar'bi loud speaker domin yin bayanin abubuwan da dramar ta k'unsa da harshen hausa. "Kamar yanda muka gani, yara ne biyu a matsayin ma'aikatan asibiti, sai kuma yarinya d'aya wacce ita ce matsayin marar lafiya, ga kuma mutum biyu a matsayin uwa da uba. Mun ga yanda aka nunar da ciwo yake addabarta, har wani lolacin take fita daga hayyacinta. Kwatsam wata rana ciwon ya tasar mata, aka kai ta asibiti domin bata taimakon gaugawa. Likitar farko ta nunar ma iyayen yarinyar cewa ai wannan yarinyar su ma cire rai da ita kawai, domin kuwa tata ta zo k'arshe. Wannan ciwon nata ba na tashi ba ne. Su koma gida da ita kawai su jira lokacin mutuwarta. A wurin gardama ta b'arke tsakanin iyayen nata, yayin da mahaifiyarta mace ta kafe a kan bata yarda da maganar likitan ba, domin kuwa babu wanda ya san gaibu sai Allah. Sannan kuma ita cuta ba mutuwa ba ce. Mahaifinta kuma ya kafe cewa lallai sai dai su koma gida, saboda shi d'in dama ya gaji da kashe mata kud'i a banza kullum ciwo sai ta'azzara kawai yake. Likitar ganin cece-kuce d'insu ya dame ta ya sa ta kore su daga ofishinta. Gida suka wuce kai tsaye, har a lokacin mahaifiyar yarinyar bata cire tsammani ba. Washe gari ta d'auke ta ta kai ta wata asibitin, inda suka tarar da d'ayar likitar can. Ta mata bayanin lalurin yarinyar, take ta gamsu da bayaninta. "Babu komai, ki kwantar da hankalinki, insha Allahu zata samu lafiya. ita cuta ai ba mutuwa ba ce, abin da nake so da ke dai kawai ki dage da yi ma 'yarki addu'a. Na miki alk'awarin kula da ita tamkar yanda zan kula da 'yata da na haifa da cikina." Sosai mahaifiyar yarinyar ta ji da'di. Haka wannan likitar ta ringa kula da yarinyar kamar yanda ta yi alk'awari. A k'arshe yarinyar ta tashi da k'afafuwanta, ta warke tas kamar bata tab'a yin ciwo ba. Sai ga yarinyar da taimakon mahaifinta, ta zama rufin asirinsa, ta zama abar alfaharinsa a k'arshe. Idan zamu auna wannan diramar, mu mata karatun ta natsu, zamu ga akwai tarin darussa a cikinta. Akwai abubuwan koyo da dama a cikinta. Mun ga yanda likitar farko ta yanke k'auna daga rahamar mahalicci, bayan kuma Allah mad'aukakin sarki maji rok'on bayinSa ne. Mun ga yanda likitar ta nuna masu tamkar ta san gaibu ne, bayan kuma La ya'lamul-gaibu illallah. Daga cikin darussan wannan diramar, mun tabbatar cewa duk inda ake ba duka ake taruwa a zama d'aya ba. Kamar yanda likitar farko ta kore su, sai gashi Allah ya had'a su da ta kirki. Ke nan dai kar mu zama masu yin jam'i ga komai, domin kuwa komai za a iya samun banbanci. Mun 'karu da ilimin lallai cuta ba mutuwa ba ce, ganin mutum yana fama da ciwo, ba shi ba ne zai sa a yanke k'auna, domin kuwa Allah'n da Ya bashi ciwon, zai iya kawo masa sau'ki a ko wane lokaci. Sannan kuma kafin a saukar da cuta, sai da aka saukar da maganinta. Duk irin ciwon da mutum yake fama da shi, kar ya zama mai gajen ha'kuri ga mahaliccinsa, ba wai rashin so ba ne ya sa ya d'ora masa cutar, a'a, yana neman ya k'ara kusanci gare Shi ne. Yanzu idan muka d'auki wani misali; zamu ga so tari mutum yana fama da ciwo, a lokacin da yake ciwon, yana yawaita ambaton Allah, sallah a lokacinsa baya wuce sa. Ba dan komai ba, sai dan yana gudun kar mutuwarsa ta zo d'aukarsa bai gyara tsakaninsa da mahaliccinsa ba. Amma idan zamu d'auko sanda baya ciwon, wata k'ila yana kwanaki bai yi zikiri ba, ita kanta sallar k'ila kullum sai lokacinta ya wuce yake yinta. Ke nan wannan jarrabtar da Allah Ya d'ora masa na ciwo, ya k'ara kusanci a tsakaninsu. Ina fatan wannan 'yar tak'aitacciyar dramar zata zama gyara a rayuwar mutane da dama wanda suka halarci wannan walima da ma wanda zasu kalla a gidajen talabijin. Duk wanda suka zo wannan wuri, Allah Ya albarkaci rayuwarsa, Allah Ya biya masa duk kanin buk'atunsa na alkhairi. Mun gode k'warai da gaske." A lokacon da Amrah ta koma mazauninta, na ga da dama daga cikin mutane wasu na kuka sosai, wasu na share hawaye, wasu kuwa kallo guda zaka masu ka tabbatar lallai jikinsu ya yi sanyi k'warai da ainun. Babban abin da ya fi tab'a min zuciya a kan bayananta shi ne; nata lalurin, yanda take fama da nata cutar a ko wane lokaci, amma a hakan ta gode wa Allah, har take nunar wa mutane muhimmacin d'aukar k'addara. A lokacin na k'ara tabbatar da rayuwar Amrah mai kyau ce, kuma abar a yi koyi da ita. Bayan an gama bayar da kyaututtuka ne aka bu'kace ta da ta fito, gwamnan jihar ya bata kyautar kujerar Makka, sannan da tarin envelopes wanda manyan mutane da dama suka aiko mata da ita. A dalilinta, an ba makarantarsu kyautar naira miliyan d'aya. Murna sosai ga mutane, Amrah wadda ke jin abun tamkar a mma farki ta kasa furta komai, da gudunta ta isa inda nake, ta min rungumar da ke k'ara shauk'i a tsakaninmu, ina jin yanda bugun zuciyarta ke tafiya dai-dai yanda ake sonshi, hawayen farin ciki basu daina sauka bisa kumatunta ba. Jin an sake kiran sunanta ya sa ta saurin sakina had'e da mayar da kallonta ga inda loud speaker ke fitowa. "Ta sake samun kyauta daga wani bawan Allah. Wanda shi ya san lalurinta, ya bada izinin duk sanda ciwon nata ya tashi, kai tsaye ta je asibitin kud'i ta Dr. Dara, ba tare da an caje ta ko sisi ba. Bawan Allah'n ya buk'aci kar a fad'i sunansa." Wani kyakkyawan hawaye ne ke sake fita daga k'wayar idonta, saurin isa matakalar ta yi, ta karb'i takardar da aka bata, wacce ita zata zama shaidarta a duk sanda zata je asibitin. Shugaban makarantar da kanshi ya mik'a mata loud speaker, cewa ta yi kalaman godiya had'e da bankwana, kamar yanda dama can haka aka tsara, ita ce zata yi su. Da larabci ta ringa zubo bayani, cikin k'warewa tamkar dama can harshenta ne larabcin, bayan ta gama ne kuma ta koma da harshen hausa. "Kalamai ba zasu iya fad'in iya halin farin cikin da muke ciki ba yau. Babban abin farin ciki a fa'din duniyar nan, shi ne yau mutum ya wayi garinsa da hardace littafi mai tsarki baki d'ayansa, sannan kuma yake amfani da shi. Mai girma gwamnan wannan jiha, mai girma wakilin sarki Mukhtar, manyan mutanen da suka halarci wannan taron, iyayenmu, yayyenmu, k'annenmu, a madadin wannan makaranta da d'aliban da ke cikinta, ina mai amfani da wannan dama domin mik'a sak'on godiyarmu. Mun gode k'warai, Alllah Ya saka da alkhairi, Allah kuma ya mayar da kowa gidansa lafiya. Mu kuma Allah ya bamu ikon amfanar da kanmu da kuma al'ummah abin da muka karanta. Rabbi Ya sa mai amfani ne a gare mu. Ba wai mun koya, mun hardace kuma mu barshi ya tafi a haka nan ba. Mu sani cewa, matuk'ar muka sake bamu karantawa, to tabbas zamu neme shi daga kanmu mu rasa. Na gode." Ta mik'a sifikar ga shugaban makarantar. Kabbara aka d'auka da k'arfi, wasu na k'ok'arin tashi domin barin wurin, wasu kuma sun bari har sai an yi addu'a sannan. Sai bayan an fara watsewa sannan Hajiya Suhaila ta zo, cikin rashin jin dad'i take shaida min abin da ya hana ta zuwa da wuri, Baban su Annur ne zai tafi Abuja, kuma bai tafi da wuri ba. Tare muka rankaya muka koma gida, ni da ita da k'annena Zulaihat da Fatima a cikin motarta, sai Amrah, da wasu k'awayenta mutum hud'u suka bi motar Annur, wanda murna ta kasa b'oyuwa daga kyakkyawar fuskarsa, yana mai matuk'ar jin dad'in wannan lokacin. Bayan mun koma gida ne mutane suka ringa zuwa yi mana murna, gida ya cika sosai kamar ana biki ko suna. D'inkuna kala biyu Hajiya Suhaila ta yi ma Amrah, masu matuk'ar kyau da tsada. Haka rabar ta kasance mana, farin ciki sosai da murna, shi kanshi Mallam abin ya k'i b'oyuwa, a k'ofar gida aka shimfid'a masa manyan tabarmi shi da 'yan uwa da abokansa. Bayan wata d'aya. A lokacin ne shugaban makarantar su Amrah ya zo har gida a kan maganar kujerar Makkarta, wai maganar ta taso, har ma an ce ta zo za a mata passport nan da kwana biyu. Sanda maganar ta riskemu a gida, sam! Amrah ta ce ita ba zata je ba. Wai sai dai ni ko mahaifinta wani ya karb'i kujerar, ba zai yiu ita ta je mu kuma bamu je ba. Daga ni har mahaifinta sam muka k'i kar'bar wannan tayin nata, babu yanda bata yi ba amma muka kartake cewa dole sai ita d'in zata je. Haka aka zo har gida aka tafi da ita da Mallam, aka yo mata passport na tafiya aikin Hajji. Saboda nan da sati bitu za a fara tafiya. _Rayuwar nan cike take da k'alubale masu girman gaske. Mafi girman jarrabta shi ne a had'a ka da ciwo. Duk wani talauci mai sau'ki ne idan kana da lafiya. Cutar sickler na d'aya daga cikin manyan cutuka, sai dai kar mu d'auki hakan a matsayin iyakar rayuwarmu ke nan, sau da dama masu lafiyar suna mutuwa su bar masu fama da ciwon. Allah Ya 'kare mu da lafiya, Ya bamu ikon cinye jarabawoyinmu._ Pinky durling💗 *RAZ 2* [8/30, 3:34 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 1⃣6⃣ Shirye-shiryen tafiyar su Amrah ya kankama sosai, har a makaranta ta yi bankwana. Sai dai kuma abin da yake ci min tuwo a akushi, sanin lalurin Amrah da na yi, tana da buk'atar mataimaki a aikin Hajji da zata yi. Yarinya mai yawan ciwo, bai kamata ta yi tafiyar d'in mako biyar ba tare da mai kula da ita ba. Duk sanda zan mata maganar sai dai kawai ta yi murmushi, ta ce, "Umma babu komai insha Allahu. kin ga ai na riga da na saba." "Kayya, Amrah ai shi ciwo baya da sabo. Sai dai addu'a kawai." Ranar da ya rage kwana biyar su tashi ne Hajiya Suhaila ta zo, take shaida min wai zata je aikin Hajji ita da Islam, sai dai su d'in ta Abuja zasu tashi, kyauta aka ba mai gidanta kujerar guda d'aya, yanayin aikinsa ya sa ya ce ba zai je ba. Shi ne ya had'a da Islam ita ya biya mata su yi tare. Duk da ba ta gari d'aya zasu tashi da Amrah ba, si da na samu kaina da kwanciyar hankaali, na ji wani sanyi sanyi a zuciyata. Shi kan shi Annur ya ji da'di sosai, a ranar ya zo mata bankwana saboda zai je Bauchi gobe, akwai wata University da ya zana, yake son zuwa don ganin yanda aikin ya kasance. Har da kuka Amrah tayi sanda zasu rabu, ji take tamkar ba zasu sake had'uwa ba. Canjin riyals ya mata na dubu hamsin, sanin ko ya bata ba zata karb'a ba ya sa ya bani cewa na ajiye mata. Na masa godiya sosai tare da fatan alkhairi a tafiyarsa. Haka lokacin tafiya ya yi muka raka ta har Hajj camp, daga can aka mana iyaka da ita, cewa za a fara kwasarsu a marcopolo zuwa Airport. Tafiyar Amrah ta zame min wani gagarumin abu, kwata-kwata hankalina ya kasa kwanciya, duk da muna waya da ita akai akai, tun daga ranar da suka dira Jidda har yau da zasu bar Birnin Madina, zuwa garin Makka. Bayan sun isa Makka ma sai da ta kira ni, a lokacin har harami ta je ta dawo. "Umma yau sai ga ni ga abin da nake gani a kallo, ka'abah. Umma ashe k'atuwa ce ba k'arama ba, amma a kallo sai nake ganinta kamar k'arama." A yanayin da ta yi maganar kawai ya isa ya tabbatar da halin farin cikin da take ciki, sosai take nishad'i. "To Amrah dama ina ta ga zama k'arama? Ki ce sai kika ga muk'ama Ibrahima." Na fa'da da fara'a sosai kamar tana a gabana. "Umma na ga muk'ama Ibrahima, sai dai daga nesa ne ban matsa inda take ba saboda cinkoso. Insha Allahu nan ba da jimawa ba zan matsa har inda take in tab'a da hannuwana." Shiru na yi jim, kafin na ce, "Amma ki kula sosai Amrah. Kin ga ke d'in ba wani girma ne da ke ba, kar a je a matse ki ki gagara numfashin kirki. Ina jin labarin yanda cunkoso yake kashe mutane fa." Murmushi ta yi mai sauti kafin ta ce, "Insha Allahu Umma zan kula sosai. Da yake ma tare muke da Maman Abba, nan d'in ma d'akinmu d'aya da su." "Allah sarki! Matar kirki ke nan. Na ji da'di sosai da Allah Ya had'a ku, dama tun a Hajj camp d'in nan na fahimci suna da kirki sosai. To ya maganar su Hajiya suhaila? Kun had'u kuwa?" "Bamu had'u ba umma. Jiya dai mun yi waya cewa sai gobe zasu zo nan Makka. Kin san su basu je Madina da wuri ba." "Haka ne." Na furta ina canza salon maganar daga wasa i zuwa ta kirki sosai, "Dan Allah Amrah kar ki manta da abin da na saka ki. Ki ma kanki addu'a sosai, Allah Ya yaye miki cutar nan, da dukkan 'yan uwa musulmai." Ajiyar zuciya ta sauke had'e da fad'in, "Insha Allahu zan yi sosai Umma. A Madina ma na yi ai." Murmushi mai sauti na yi, "Allah Ya karb'a to. Da duk wata addu'a da ta dace ba sai na fa'da miki ba. Ki gaishe da maman Abban, sai anjima." Na tsinke wayar. Haka Amrah suka yi ibada sosai, kamar yanda nake ji daga Maman Abba a duk lokacin da muka gaisa da ita, tana yawaita fad'a min, "Gaskiya Maman Amrah kin yi sa'ar 'ya, mai hankali, tarbiyya da kuma ilimin addini. So tari idan wani abu ya shige min duhu, ita take tunasar da ni, da duk sauran 'yan d'akin ma. Bata wasa da zuwa masallaci, duk irin laziness d'in da nake ji a kan zuwa masallaci, ita zata kwantar da kalamanta, ta sanyaya min jiki, wanda dole sai na je masallacin. Baccinta k'alilan ne, tana raba darenta da nau'ukan ibadu, wanda ko a cikin manyan mata da suka gama mallakar ilahirin hankulansu, ba lallai a samu kamarta ba. Na matuk'ar jin dad'in shigowarta duniyata, ta gyara min kurakuraina cikin hikima da fasaha, yanda ba zan tab'a jin haushinta ba. Ta tunatar da ni abubuwa da dama, wanda ba llallai ba ne na tuna su a duniyata. Ina mai k'ara jaddada miki maman Amrah, ki k'ara gode wa Allah da kyautar Amrah da Ya baki." A dai-dai lokacin da ta kai aya a zancenta, na murmusa cike da jin dad'in kalamanta, had'e da furucin, "Alhamdulillah." A tak'aice. Jin Amrah ta karb'i wayar ya sa na ce, "Sai anjima Amrata, a yi ibada sosai." "Insha Allahu, Ummah. 'Yan jirgi na farko ma har an saka su yin d'awafin bankwana." "To madallah. Sai anjima." Cike da jin dad'in kalaman Maman Abba na ajiye wayar bisa kujera. Ni kad'ai ke sakar ma kaina murmushi. Ko da maman Abba bata fad'i ba, na sani, na san cewa na yi sa'ar 'ya, abar alfahari, wacce zata iya rayuwa a duk duniyar da zata tsinci kanta, ko da ni ko babu ni. Murmushi bai fice daga fuskata ba na ji salllamar Annur, amsa masa na yi da murmushin da ban kawar da shi ba. "Maraba da Annur." Na furta had'e da mik'ewa na bashi wurin zama. Bayan mun gaisa ne yake shaida min jiya ya dawo daga Abuja, maganar sabon ginin da zai ma kamfanin magani na dana, sabon reshen da zasu bud'e a garin Minna. Fatan alkhairi na masa, sannan ya zaro kud'i naira dubu goma ya ajje min, "Annur baka gajiya ne wai? Wasu lokutan har kunyarka nake ji, wasu lokutan na kan ji ina ma zaka duba zuciyata ka ga yanda nake ji a duk sanda zaka yi min kyauta? Na so dai a ce abin ya tsaya a tsakanin kai da Amrah kawai." "Bana son jin haka daga bakinki Umma. Ko kin manta cewa ni ma d'anki ne kamar Amrah? A ganina, duk abin da zan iya yi ma Momy ba tare da haufin komai ba, haka zan miki shi ba tare da wani abu ba. Please and please Umma, ki d'aukeni tamkar yanda na da'uke ki, ki bani matsayi kamar yanda na baki. Ki daina k'o'karin dakatar da ni daga kyautata miki." Sai a sannan ya dakata da maganarsa, yana mai duk'ar da kansa k'asa. Ajiyar zuciya na sauke, "Haka ne Annur. Kar ka tab'a tunanin akwai wani banbanci a tsakaninka da Amrah. Yanda take tawa haka kaima kake nawa. Allah ya maka albarka ya taimake ka a kan duk k'udururrukanka na alkhairi." "Har na ji dad'i Umma. Bara in tashi. Su momy ma gobe muke tsammanin dawowarsu." cikin Mamaki na ce, "Tun da wuri haka? In ce ko su Amrah sun riga su tafiya?" Bayan ya mik'e tsaye ya ce, "Sun riga su kam. Kin san yanayin tafiyar tasu ba d'aya ba. Su ta can b'angaren tuni aka fara kwasar Alhazai, tun sallah da kwana hud'u." Mi'kewar na yi ni ma na ce, "Allah Ya dawo mana da su lafiya. Sai anjima." Bayan kamar sati d'aya su Amrah suka dawo, sosai na yi mamakin yanda ta koma, ta yi b'ul-b'ul gwanin sha'awa kamar ba ita ba. Ta yi kyau matu'ka, ciwo kuma dama tun da ta je sau d'aya kawai ya taso mata, kuma Hajiya suhaila da Maman abba suka kai ta Saudi German, inda aka bata treatment mai kyau, suka kula da ita, suka killace ta har sai da suka ga ta murmure kamar ba ita ba. Har da hak'orin Makka na zinari ta saka, wanda ya haskaka hak'oranta, ta sake cika sosai. Sosai Annur ya yi farin cikin ganinta, wanda a ranar da ta dawo ya d'ora idanuwansa a nata, ya shiga wani irin hali mai wuyar fassara, duk irin dod'ad'diyar k'walwar mutum dole ya fahimci halin da suke ciki, dole a ga tsantsar kewar ganin fuskokin junansu da suka yi, na tsawon kwanaki talatin da takwas. A cikin wannan rana ne Annur ya furta mata kalmar *"I LOVE YOU AMRAH."* Kalmar da bata tab'a shiga tsakaninsu ba tun da suke, saboda ita Amrah har a lokacin gani take kamar ba son soyayya take ma Annur ba, kamar sha'kuwa ce kawai a tsakaninsu. Sai dai kuma jin kalmar da ta fito a tsakanin lab'bansa, ya sa ta kasa gasgata kanta, take jin wani sabon yanayi a duniyarta. *Sai yanzu, Annur? Duk iya zamanku da Amrah sai yanzu ka iya furta mata wannan gagarumar kalmar, wadda baka tab'a furta ta ga kowa ba?* *Masha Allah! Hakan ya yi kyau ai.* *Ina team Amranoor? Abin da kuka jima kuna tsumayi ko? To yau dai ta faru, sai kwasar rawa ke nan.* *Wiyara wattpadians? Simply search PrincessAmrah. Vote and comment on each line, I'll be glad if you do so.* Pinky durling💗 *RAZ 2* [8/30, 3:35 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 1⃣7⃣ Tun daga lokacin da soyayya mai 'karfi ta gama shiga tsakaninsu, zuciyata take ciki da farin ciki. Sosai ciwonta ya yi sauk'i kuma, tun daga sanda suka dawo daga Saudiyya, har yanzu. Yanzu haka Amrah ta shiga SS2 ne har ma sun kusa shiga 3, Annur kuma ya samu aiki a wani babban kamfanin k'ere-k'eren motoci da ke Birnin Abuja, yana masu aiki ta b'angaren zane-zane. Hajiya Suhaila kuma ta samu Dady'n su Noor da maganarsa shi da Amrah, bai hana ba, saboda shi dama babban burinsa dai yaransa su ginu bisa tafarki mai kyau, su samu ingantaccen ilimi wanda zasu amfana da shi, kuma ya yi alfahari da su. Kuma Noor d'insa ya samu. Dan haka ba zai hana sa auren duk wacce ransa ke so ba. A lokacin da ta shiga SS 3 ne aka fara maganar aure, har ma manya sun shiga maganar. Har a tsawon wannan lokacin Amrah bata daina tunanin mutumin da ta yawaita gani a asibiti cikin keken guragu ba, bata daina mamakin mutumin ba, sau da dama ta kan same ni da maganar, "Umma na rasa yanda zan yi na cire wancan mutumin daga zuciyata. A duk sanda zan zauna ni ka'dai, ya kan fad'o min a rai. Na rasa ko shi d'in waye, ban tab'a ganin kama irin tasu ba." "Ba abun tunani ba ne wannan ba Amrah. Kin san a duniyar nan ana kama, akwai wanda kai kanka idan ka kalle shi zaka san kuna kama, kuma a zahirin gaskiya baka had'a komai da shi ba. Dan haka ki daina wannan tunanin. Annur d'inki dai shi ne kawai, kuma insha Allahu shi zaki aura." Da kunya ta duk'ar da kanta k'asa, tana wasa da yatsun hannunta. Kud'in neman auren Amrah kansu dubu d'ari biyu aka kawo, a raina har ina jin kamar sun yi yawa. Haka kayan saka rana da aka kawo, komai a wadace, katan katan d'in abubuwa haka aka ringa dire su a tsakar gidanmu. Wata bakwai aka saka auren, wanda ya yi dai-dai da gama makarantarta. Daga sanda aka kawo kayan saka rana, kafin a raba su sai da ta yi saukar Al-Qur'ani, tana fatan Allah Ya saka albarka a rayuwar da zata tsinci kanta, rayuwar da take yawan tunanin fad'amawa, take jin ina ma a ce a gidansu zata yita zama ko bayan auren. Ko kad'an bata son abin da zai raba ta da gida. Duk sanda zan yi wata tafiya zuwa garinmu, kafin in dawo sai ta yi ciwo, ba wai ciwon sikilarta ba, ciwon rashi na a kusa da ita kawai. Saudiya ma da ta je ashe daga farko sai da ta yi, daga baya ne ta koma dai-dai. To bare kuma yanzu da zata tafi ta bar ni, bari na har abada. Zata fad'a wata sabuwar rayuwar, mai cike da k'alubale. Ba wai Amrah kad'ai ba, ni ma kaina da na haife ta dan dai aure ya zama dole ne. Har ji nake a raina 'Banda aure ibada ne, me zai sa ka haifi 'yarka, ka raine ta tun tana 'karama, ka so ta, ta so ka, amma rana d'aya wani ya raba ka da ita?' Hawaye nake ni kad'ai a duk sanda na keb'e, nake irin wannan tunanin. Ya zan yi da tunanin Amrah bayan barinta gida? Ya zan yi na cire tunaninta daga zuciyata? Wane hali zata ringa shiga a duk lokacin da ciwonta ya taso? Sauk'in ma d'aya, bani da haufi ko kad'an a rayuwar da zata fad'a. Bana haufin wanda zata yi rayuwa a k'ark'ashinsa. Na tabbata zai kula da ita, tamkar yanda zan kula da ita. Zai nuna mata soyayya, fiye da yanda ni zan nuna mata. Zai bata ingantacciyar rayuwa, fiye da yanda ni zan bata. Sallamar da Amrah ta yi ce ta dakatar da ni daga duniyar tunanin da na lula, "Umma, ke kad'ai?" Ta furta had'e da zama kusa da ni. Murmushi na k'irk'iro had'e da furta, "Ni kad'ai fa. Ya makarantar?" "Makaranta lafiya k'alau Umma. Yanzu ma Mallam yake fad'a min wata musabak'a da ta taso. Wai za a yi ta nan da wata biyar, ta k'asa ce. Kin san ni na wakilci jihar Katsina waccan shekarar, har na zo ta biyu. To yanzu a cikin mu ukun da muka zo farko ne aka d'auke mu, mu za a had'a da mutum uku da suke ko wace jiha, idan an had'a mu a nan ma wata gasar ce, wanda suka zo farko ciki za a fitar da wanda zasu wakilci Najeriya." "To fa!" Na jinjina kai. "Abun na yi ne ashe. Ba dai sai an k'ara k'unshe ku ba wannan karon ma ko?" Murmushi ta yi bayan ta mik'e tsaye, ta cire hijabin jikinta. "Ba za a 'kunshe mu ba umma. Wancan ma dan muna da yawa ne sosai, akwai wanda suke da bu'katar gyara sosai a karatunsu. Amma wannan mu uku ne kawai, ni ce ma kawai fa daga islamiyarmu, sauran mutum biyun kowa da tasa makarantar." "Yauwa to, yanzu na ji magana. Allah Ya taimaka Ya sa a yi a sa'a." "Ameen Umma." Ta fura tare da shigewa cikin d'aki. Babu jimawa kuma ta fito, fuskarta babu annuri ta ce, "Umma, wai kuma yanzu Mallam Kamala ya kira ni, wai akwai wani wa'azin aure da aka gayyace shi ba zai samu damar zuwa ba, wai in taimaka in wakilce shi. Umma wallahi ni ban shirya ma wa'azi ba yau, bare kuma na aure wanda dole sai an tsara komai." Ta dafe kanta had'e da zama. Kad'a mata kai na yi, fuska d'auke da murmushi na ce, "A'a 'yata. Bana son jin hakan daga gare ki. Malaminki fa ne ya buk'aci ki taimaka masa." Ajiyar zuciya ta sauke, "Ba wai bana son yi ba ne Umma, shirya masan ne dai ban yi ba. Kyau a ce tun jiya ya sanar da ni, ko kuma islamiyyar safe. Amma sai yanzu da azahar ta kusa ne zai fad'a min? Wai kuma da la'asar ake son in fara?" Dafa mata kai na yi, cike da bata k'warin guiwa na ce, "A hakan dai zaki daure ki yi. A cikin mutum nawa da ke makarantar, ya ware ki ke kad'ai ya ce ke zaki wak'ilce sa? A ganina ai wannan ma abin alfahari ne, ko?" Bata son jayayya da ni ko kad'an, a bata so d'in ta hak'ura, ta d'auko takarda da biro ta fara rubutu. Ko da la'asar ta yi ta gama shirinta, dama ya turo mata inda yake son ta je d'in. Hijabinta ta saka har k'asa, mai kalar ruwan toka. Mai hannu ce, hakan ya bata damar fiddo tafukan hannyenta a waje, ta rataye k'aramar jakarta, ta d'aura ni'kabinta, sannan ta min bankwana. Fatan alkhairi na mata, sannan mahaifinta ma da ya dawo dai-dai lokacin ya mata, ta tafi. Daf da magrib sai gata ta dawo a rikice, tamkar wacce bata cikin hayyacina. Kallo d'aya zaka mata ka tabbatar bata cikin natsuwarta, kamar akwai wani abu na tashin hankali da ta gani. Tambayarta nake me ke damunta? Me ya same ta? Amma ta kasa furta min komai, kallona kawai take tana zazzare ido. Salati nake ina mai k'ara dubanta, duba ta tsanaki na ce, "Zauna ga tabarma nan. Ki natsu sosai sannan ki min bayani." Bata musa min ba, zaman kuwa ta yi, ta had'e kanta da guiwoyinta, ga jikarta a ma'kalk'ale da ita, sai nik'ab d'inta a d'ayan hannunta. Dama na bata sosai ta samu natsuwa, har sanda aka kira sallah na zuba mata ruwa a buta, ta tashi ta gabatar da sallar. A dai-dai gamawarta Mallam ya dawo, bayan ya zauna ne ta fara bamu labari. "Umma, yau na had'u da tashin hankalin da tun da nake a rayuwata ban tab'a shiga irinsa ba. Na ga abin mamaki, wanda tun da nake ban tab'a ganin irinsa ba. Umma na kasa gasgatawa, shi ne, ko ba shi ba ne? Na kasa amincewa, shi d'in ne dai ko kuwa wani mutumin ne na daban?..." tana kaiwa nan ta yi shiru a zancenta, ta dafe kanta da ke barazanar fashewa, ta ci gaba da fad'in, "A dai-dai sanda na gama wa'azi, k'arfe biyar da rabi na baro gidan, amaryar da k'awayenta suka rako ni har bakin titi, suka tsayar min da keke napep sannan suka bani dubu uku. Keke nalep d'in to ba mai tuk'in bane kawai zaune, su biyu ne har da wani a gefensa. Duk da na yi addu'a sanda zan bar gida, na yi addu'a bayan fitowata daga gidan da na yi wa'azin, sannan kuma na yi addu'a a dai-dai sanda zan hau napep d'in. Na samu kaina da rashin natsuwa, gabana sai fad'uwa yake ban san dalili ba. A titin ring road da ya kamata mu yi gabas daga shi, sai na ga sun zarce da ni. Ganin haka ya sa na ce, "Mallam, Gidan dawa fa na ce ku kai ni." Daga mai tuk'in har na kusa da shi babu wanda ya furta min komai, babu wanda ko da kallona ya yi. Sai ma k'ara wutar napep d'insu da suka yi. Salati nake ina ambaton sunan Allah, hankalina baki d'aya ya gama tashi, sai faman kalle-kalle nake. Wata kwana na ga sun shiga da ni, daga nan suka ringa shiga lungu da sa'ko, har muka b'ulla wani k'asurgumin daji, wanda tun da nake a rayuwata ban tab'a sanin akwai irin wannan dajin a Katsina ba. A dai-dai bakin wata gidan gona suka dakata, wanda ba shi ne ke tu'kin ba ya fara sauka, sannan wanda yake tuk'in ma ya sauka. "Wai bayin Allah ina ne nan kuka kawo ni? Dan Allah ku rufa min asiri, ku taimaka ku fitar da ni daga wannan dajin." Dariya suka k'yalk'yale da ita su duka biyun, kafin suka finciko ni da k'arfin tsiya daga napep d'in, suka isar da ni cikin gidan gonar. A wani babban falo suka dire ni, ina kuka sosai, kuma har a lokacin ban manta da sunan Allah ba, ban daina neman taimako daga mahaliccina ba. Cikin wani d'aki suka shiga, sai ga d'ayan ya dawo, d'ayan kuma bai fito ba. Wanda ya fito d'in ne na ji yana waya, wayar da ta tayar min da hankali, ta sa gabana ya ringa duka da sauri-sauri. "Oga mun zo kuma baka nan sai Yax kawai muka samu. An samu wata d'anya shakaf. Uztaziya ce sosai, dan fuskarta ma a nad'e take da nik'ab, ina jin a jikina zata maka sosai. Ehh zata maka sosai ma kuwa." Ya k'arasa wayar da dariya a fuskarsa. Bayan wasu da'kik'u wanda ba zasu wuce goma ba, sai ga Ogan nasu ya iso, fuskata na kallon wata k'ofa ta inda wancan d'ayan ya shiga, har ya iso daf da ni ban sani ba. Hakalina bai gama tashi ba, ban daina jin fargaba ba, sai a lokacin da idanuwana suka fad'a a saman fuskarsa. Shi d'in kanshi da mamaki yake kallona, "Ke ce?" Ya furta had'e da zaro ido. Mik'ewa na yi ina gwada sa da yatsa, ido da bakina duk a bud'e suke, "Kai....kai ne Ogan nasu dama?" *To fa! Me ke faruwa ne haka? Wanene wannan Ogan wanda suke satar 'yan mata? Me yasa yake mamaki dan ya ganta, hakan na nufin ya santa ke nan? Ita d'in ma da alama ta sanshi fa. What is happening? What do you think, readers?* *Duka zaku samu wannan amsoshin a next page insha Allahu.* _kar mu manta da ambatar sunan Allah a duk halin da zamu tsinci kanmu. Mu daure mu kira sunan mahaliccinmu, saboda shi ne kad'ai zai iya bamu kariya, zai kub'utar da mu daga halin da muka tsinci kanmu._ *Wattpadians, don't forget to comment on each line, and then vote after reading every page. Ina kallonku, masu karantawa basa voting, Ghosts ke nan. PrincessAmrah zaku yi searching don samun many books of mine. Thanks always* Pinky durling💗 *RAZ 2* [8/30, 3:35 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 1⃣8⃣ Sunkuyar da kansa ya yi k'asa yana mai murtsuka gashin kansa da duka yatsunshi. Jin k'afafuwana kamar suna neman gagarar d'aukar gangar jikina yasa na gaggauta zama da k'arfi, idanuwana suna masu kawo ruwa. "Esien!" Ya k'wala ma d'aya daga cikin yaran nasa kira. Da hanzari sai ga d'aya daga cikin wanda suka sato ni ya wanzu a gabanshi, cikin wata murya ya ce, "A mayar da ita, ta kwatanta maku gidansu ku kai ta, bana so ku mata wani abu kuma." "An gama Oga." Ya furta had'e da komawa 'daki ya kira d'ayan abokin nasa. "Kar'bi wannan takardar, daga nan ku tsaya chemist ku siyo min wannan maganin, har yanzu ina jin ciwo a k'afafuwan nan nawa, ina sauri ne ban tsaya na siyo ba." Kar'ba ya yi sannan ya juyo da kallonsa gare ni, da alama cike yake da mamakin yanda Ogan nasu ya bijirewa tayinsu, shi d'in da a kullum yake jin dad'i idan ya ga yarinya budurwa, musamman kamilallu, wanda a ganinshi su ne zai samu zumarsu yanda yake so, ya lashe zumar cike da jin da'di, a 'karshe ya b'atar da su ba tare da sun san inda kansu yake ba. "Mu je." Muryarsa ta dirar min a kunne, bayan tsawon lokacin da na lula a birnin tunani. Bin bayansu na yi kai tsaye muka doshi waje, a daidai k'ofar fita ya dakatar da ni, "Kar maganar nan ta fita matuk'ar kina son numfashinki." Kai kawai na jinjina masa, har a lokacin ban daina ruwan hawaye ba. Napep d'in na shiga, bakina bai daina addu'a ba, tunani da k'wak'walwata basu daina tababa a kan abin da na gani ba. A cikin napep d'in ne abokan suke fira, duk da halin da nake ciki, duk da rabin hankalina baya tattare da ni, hakan bai hana ni mayar da hankalina gare su ba. "Baabaa amma fa na yi mamakin Oga. Gashi dai abin da ya fi so, amma bai yi tsiyar ba." Dariya wancan di'n ya k'yalk'yale da ita, "Ina ganin dai ciwon k'afar nasa ne ya motsa. Baka ji har da magani ya ce mu siyo masa ba? Da alama shi ya sa ya sallame ta." D'ayan ya ce, "Zan iya yarda da hakan kam. Duk soyayyarsa da son falle sababbi dal a leda, amma ya bar garab'asa. Gaskiya Oga Sans akwai damuwa a tattare da shi." Baki na bud'e ina mamakin sunan da suka k'ira sa da shi, ina mai jinjina sunan 'Sans' a bakina. To waye shi? Wannan wane mutumi ne wanda kamanninsa iri d'aya da Yaa Noor d'ina? Duk ta k'are shi ne wanda na yawaita gani a asibiti. Shi ne wannan gurgun da nake gani a keken guragu tsawon shekaru da dama da suka gabata. Amma kuma ta ya zan gasgata cewa ba Yaa Noor d,ina ba ne bayan kamar tasu babu banbanci? 'Ta d'abiu da sa'banin halaye.' Wani sashe na zuciyata ya bani wannan amsar. "Ke mun zo Gidan dawa. Ta ina zamu bi?" Muryar gardawan ta dawo da ni daga duniyar da bani na kai kaina ba, duniyar da tunane-tunane ce kawai ta jefa ni. "Kwanar gaban shagon can zaku shiga." Na fad'a da disasshiyar murya, wacce kuka ya gama dishasarwa. Har gaban gida suka kawo ni, suka kuma k'ara bige min warning a kan kar maganar ta fita, kar na bari hukuma ta shiga, saboda komai zai iya faruwa da ni." Amrah na kai wa wannan gab'ar ta dakata, tana shesshe'kar kuka sosai, jikinta sai faman rawa yake. Cike da tashin hankali na jawo ta a jikina, ni d'in ma kukan nake sosai. "Ya isa haka to. Ai gashi babu abin da ya same ki ko? K'arfin addu'a ke nan." Ni d'in ma ban daina kuka ba. "Gaskiya ba za a bar maganar nan ba. Ya zama dole hukuma ta shiga wannan maganar, ko dan gaba." Mallam ya furta yana mai jinjina lamarin. "Dan Allah Abba kar a shigar, wallahi ina tsoro." Ta fa'da cike da muryar kuka. "To ke ya kike ganin gaskiyar lamarin? Ni dai na tabbata ba Annur ba ne, na san Annur yaro ne mai hankali, yaro ne mai sanin ya kamata, wanda na yi imani da Allah ba zai kasance mai irin wancan halin ba. Ga kuma babbar hujja, wancan d'in ma da kike fad'i gurgu ne, kuma ga wannan ma maganar ta kusa zuwa d'aya. Da alama dai kama ce mai tsanani suka yi. Kin san ana samun irin haka." Cike da gamsuwa Amrah ta jinjina kanta, "Na yarda da wannan bayanin Umma. Tabbas na san ba Ya Noor d'ina ba ne. Kuma dan ya nunar da alamun mamaki a lolacin da ya gan ni bai zama hujja a ce shi ba ne, tun da shi d'in ma na san shi a asibiti, shi ma ya san ni, mun sha had'uwa da shi, har gaishe ki ma yana yi. Da alama dalilin da ya sa ya sallame ni ba tare da ya min komai ba ke nan. Wallahi na yarda ba Hammana ba ne, wancan mutumin banzan dai ne. Fasi'ki, mazinaci, azzalumi!" Ta k'arisa da share hawayenta. "Mallam tun da dai abun haka ne, kuma shi d'in bai mata komai ba, kawai mu hak'ura, mu barsu, akwai ranar da zasu ha'du da dai-dai ya su." "Haka ne. Allah Ya tsayar nan to. Allah kuma Ya k'ara karewa." "Ameen ya Rabb. Kuma sai fa da ta nunar da bata son tafiyar, kamar ta san abin da zai faru. Ni na tilasta mata tafiyar, ashe abin da zai faru ke nan." Wani kukan ya sake kufce min. "Ya kamata ku yi shiru haka nan. Babu abin da addu'a ta bari. Kuma na yarda cewa addu'ar da ta yi ne ya sa abin ya tsaya nan, har zuciyarsa ta sanyaya, ya iya tuna ma ya ta'ba ganinta. Kin san mafi yawancin mutanen banza irin wa'innan, sun fi d'aukar mummunan hukunci a kanka ma sanda ka nunar da ka sansu. Amma hikima irin ta Allah, da taimakonSa sai suka sallame ta. Lallai babu k'arfi babu dabara face a wurin Allah ma'daukakin sarki! Shi ya halicce mu, shi muke bautamawa, kuma shi ne maji k'anmu. Shi ne mai taimakonmu a duk lokacin da Ya ga dama. Shi ke kare mu a duk sanda muka nemi kariyarSa. Babu babban butulci sama da neman taimako ko kuma agaji ga wanin Allah. Sau da dama wasu sukan butulce, su nema taimako ga d'agutu, wanda shi d'in kanshi sai Allah ya bashi iko. Me zai hana duk sanda muka samu kanmu a cikin tashin hankali, mu ambaci "INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN!"? Ita ce kalma mafi girma, wacce ya kamata mu ambata a duk sanda wani tashin hankali ya riske mu. Kin kyauta sosai y'ata, kin buk'aci taimako ga Allah kuma Ya taimake ki. Ina alfahari da ke, ina alfahari da baki d'aya halayenki, ina alfahari da iyalina." Ya 'karashe maganar da murmushi shimfi'de a saman fuskarsa. Take muka manta da duk wani tashin hankali, muka ci gaba da rayuwarmu kamar kullum, tana min labarin yanda wa'azin auren ya kasance. Tun daga wannan tashin hankalin da muka shiga, bamu sake samun kanmu da shiga wata damuwa ko matsala ba, Annur kuma dama na fad'a ma Amrah ko da wasa kar ta masa tad'in. Tun da dai mun tabbatar cewa ba shi ba ne, kawai dai mai kama da shi ne. Na tabbatar idan muka fa'da masa ba zai ji dad'i ba, kuma zai yi bincike sosai har a gano mutanen, bayan kuma mun saki maganar, gwara dai mu barsu da duniya, saboda ta fi bagaruwa iya jima. Haka kwanaki suka ci gama da gudanya, har su Amrah suka fara zana jarabawar WAEC. Ranar da suka fara ne ta dawo cikin yanayin zazzab'i, irin mai zafin jikin nan sosai, wanda ko rintse idonta cikin wani hali take yinsa. Mallam Mu'ammar ne da kanshi ma ya dawo da ita bisa mashin d'insa, bayan sun fito daga exams. A yanayin da na ganta, sai da hankalina ya tash, gabana ya ringa fad'uwa. "Me ya faru da ke?" Na gaggauta tambayarta. Tab'a fatar jikinta da na yi ne ya bani amsar tambayar da na mata, tun kafin ita d'in ta amsa min. "Subhanallahi! Lafiya lau fa kika fita Amrah. Ko kin shiga ruwan saman nan da aka yi ne" A daburce na sako zancen, ina mai sake tab'a jikinta. "Umma an caccanza mana hall ne har sau uku, daga farko aka kai mu Class, sai aka sake canza wani, a 'karshe kuma aka kai mu exam hall. Kuma duk a cikin ruwa muka yi yawon. Tun daga sannan ne na ji jikina ya mutu, zazzab'i mai zafi yana sauko min, da k'yar ma na rubuta jarabawar." Ta k'arisa maganar tana mai yin hamma, irin mai nuna yanayin zazzab'in nan. "Aikam tashi zaki mu tafi asibiti, tun da wuri ma.." ban rufe baki ba muka ji sallamar Annur. Sanye yake da suites ba'ka'ke, sai light blue riga mai dogon hannu daga k'asa, neck tie di'nsa bak'i mai di'go di'gon light blue d'in. Amsa sallamar tasa na yi, ina mai k'oka'rin k'irk'iro masa murmushi. Bayan mun gaisa da shi, Amrah ma ta gaishe shi ne yake tambayar lafiya? Dan ya kula da yanayin namu. "Ehh to, ta dawo exam ne ka ga ko uniform ma bata cire ba. To kuma zazza'bi take sosai, ga hawaye nan sai fita suke da kansu. Yanzu haka shawarar kai ta asibiti ma nake." Kallonshi ya miyar ga Amrah, cike da soyayya, kallo mai nuna zallar tausayi, k'auna da kuma irin kewarta da ya yi. Kalar idanuwan nasa ne suka sauya, daga farare tas da suke, zuwa jajaye. Haka yake, a duk sanda zai tarar Amrah bata da lafiya, kuka ne kawai baya fasawa. Cikin wata irin murya ya ce, "Ta shirya zan kai ta Umma." Maganar da ya yi ce ta sa na tuno zancen da nake so mu yi da shi, wanda na jima ina yi masa amma ya yi kunnen uwar shegu da ni. "Yauwa, Annur ba dai zan gaji da rok'onka ba, dan Allah..." Saurin dakatar da ni ya yi, "Wallahi Umma bana jin zan iya yin awon genotype. Ina ji a jikina ni ba AS ba ne, AA ne da ni. Ban san ya zan yi ba idan na yi wannan awon aka ce ina da AS, ban san wane hali zan shiga ba. Bana jin kasantuwar Amrah SS zai sa na hak'ura da aurenta." Gya'da kai na yi ina kallonshi. Cikin k'wayar idonshi na kalla, na karanci yanda soyayya ta makantar da shi, ta sa baya ganin komai sai Amrah. Soyayya ta kurumtar da shi, ta sa baya jin maganar da nake masa a kan wannan awon. Sosai na fahimci yanda soyayya ta jirkitar da tunaninsa, ta sa ya kasa gane muhimmancin wannan awon. "Amma Annur, baka tunanin halin da yaranku zasu shiga nan gaba? Me kake tunani idan yaran da kuka haifa suka shiga cikin hali irin na Amrah, ko kuma ma wanda ya fi nata?" "Wannan ba abun damuwa ba ne Umma. Zamu iya tsaida haihuwar ma baki d'ayanta. *AMRAH NAKE SO* ba wai abin da zata haifa min ba. Wallahi ko AS nake da shi ba zan iya hak'ura da ita ba. Bana jin zan yi rayuwa mai kyau ba tare da Amrah ba. Bana jin zan ta'ba yin aure matu'kar ba Amrah na aura ba. Saboda haka, Umma, awon genotype bashi da wani tasiri a gare ni. Dan Allah yau dai a tsayar da maganar nan. Tun kafin a saka ranar aure muke yinta, Umma ta gagara k'arewa, har gashi yanzu bai fi mana watanni uku a d'aura aure ba." Jin ya dakata daga nan, ya sa na dafe kaina, baki da'ya jikina ya yi sanyi. "Ai shi ke nan. Amrah tashi mu tafi. Bara na d'auko makullin gidan a d'aki. Amma ki fara kiran Abbanki ki sanar masa." _Addu'a na sauk'ak'a masifu da bala'iku sosai. A duk halin da zamu tsinci kanmu, na ciwo ne ko kuma wata damuwa, kar mu manta da INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN!_ Pinky durling💗 *RAZ 2* [8/30, 3:36 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 1⃣9⃣ Bayan mun isa asibitin ne muka buk'aci a had'a mu da Dr. Xarah ko kuma Dr. Rabiatu, amma aka shaida mana Rabiatu bata nan, dole sai dai Dr. Xarah. Bayan mun shiga Ofishin nata, kallo d'aya ta ma Amrah ta tabbatar da bata jin dad'i. "Sannu Amrah." Ta furta cike da tausayi. "Jikin dai kuma" ta jinjina kanta. "Wallahi kuwa Dr. Daga makaranta ta dawo min haka. Wai ruwa aka saka suka shiga wurin canjin hall, har ruwa ya mata duka." "Subhanallahi! To Allah Ya kyauta gaba." Ta zaro lokar dake gaban teburinta. "Ungo thermometer, ki saka a armpit d'inki." Karb'a ta yi kuwa ta saka, ta d'an jima kafin ta nemi ta fiddo ta. "Subhanallahi! Temperature d'inta har ya haura ma 47. Lallai zazza'bi ya shige ta sosai. Bara na rubuta mata magani. Ku tsaya ku karb'a sannan a mata awon jini, idan ya sauka dole a tarbi abun, a mata k'arin jini." Ta hau rubutu. Bayan ta gama ne ta mik'o min takardar, tare da yi mana fatan alkhairi. Har zan fita ta dakatar da ni, "Maman Amrah wai yaushe ne ma aurenta?" Murmushi na yi na ce "Wata biyu ne da 'yan makwanni suka rage. Insha Allahu idan ya matso zan zo na sanar miki." "To Allah Ya kaimu. Ina fatan dai an san genotype d'in angon nata." Ta furta a hankali. Kallona na mayar ga Annur, ina k'ok'arin magana ne ya yi caraf ya ce "Ehh, an yi Dr. AA ne da shi" "To masha Allahu. Haka ake so ai." Ta fad'a. Bankwana muka mata sannan muka fita. D'akin magani muka fara zuwa aka bata, sannan muka nufi laboratory domin awon jini. Bayan an gama auna mata mun fito, Annur ya ce, "Umma bari dai na je a min wannan awon, ba dan komai ba sai dan na tabbatar, idan AS gare ni tun wuri sai na san hanyar bi domin tsayar da haihuwa, duk da dai jikina baya bani hakan." Ajiyar zuciya na sauke, "Haka Nake so Annur. Bari mu jiraka a can har ka dawo." Ya tafi, mu kuma muka zauna jiransa. Kusan awa d'aya ya da'uka sannan ya dawo, fuskarsa k'unshe da murmushi, farin ciki ya gagare b'oye kansa. Hannunshi d'aya rik'e da takarda, d'ayar kuma a cikin kansa yana wasa da sumar kansa. Tun daga nesa yake furta, "Umma kin gani ba, dama na fad'a miki." Bayan mun mik'e taye na ce, "AA gare ka ke nan?" Ni d'in kaina ina murmushi. "AA gare ni Umma, kar'bi takardar ki gani." Bayan na duba ne na tabbatar da maganarsa. Da gaske abin da ya fad'a. Wani irin dad'i na ji ya kewaye ilahirin zuciyata, na kalli Amrah da ita kanta da'din ne ya mamaye ta. Da farin ciki muka isa gida, wanda sai da muka biya ta Crispy ya mana take away na abinci da lemo kafin muka isa. *** Rayuwa ta ci gaba da tafiya, kwanaki na gudanya, muna 'kara kusanta ga Allah, har Amrah suka gama jarabawarsu duka, WAEC DA NECO d'in. Wata da'ya kacal ya rage aurenta. A iya wannan lokacin har lefenta an kawo, akwati saiti biyu, da kaya na ji da fad'a, zan iya cewa tun da nake a rayuwata, ban ta'ba ganin kayan lefe kamar na Amrah ba. Sadakinta naira dubu d'ari aka kawo, komai dai sai hamdala. Fatana a ko da yaushe, shi ne Allah Ya kawo farin ciki a rayuwar auren Amrah. Yanda Hajiya Suhaila ke nuna mata gata da soyayya, ina fatan d'orewar hakan har gaban abada. Saitin kayan d'akinta da Mallam ya siya mata masu kyau, ba wasu na 'karya ba ne sosai, iya k'arfinsa ya yi, kuma a hakan ya samu rufin asiri. Komai ya yi kyau sosai. A makuna hud'un da ya yi saura na auren Amrah, babu abin da bamu gama ha'dawa ba. Hatta da kayan abincin da za a ci lokacin aure mun gama had'awa. Kayan kitchen d'inta bakin gwargwado mun had'a mata. Dama 'yan uwana sun had'a min gudunmawa tun watan da ya gabata sun bani, da su na 'kara na mata siyayyar kayan kitchen d'in, kayan 'yan gayu, wanda na san mai rayuwar Abuja zata iya buk'ata. Dama kuma sun ce kayan kitchen ne kawai za a tafi Abuja da su, kayan d'akinta a nan Katsina zata barsu, gidansu wanda zasu ringa sauka idan sun zo. Abujan babu abin da basu zuba mata ba. Da murna ta shigo cikin gida, bayan ta cire hijabinta ta zauna kusa da ni. "Fuskarki ta bayyanar da farin cikin da kike ciki. Da alama an faranta miki rai." Da murmushi ta ce, Umma, sati mai zuwa zamu tafi Sudan, kin san na fad'a miki a can za a yi musabak'ar k'asa da za a yi. Umma ni na haye a duk fad'in ka'sar nan, ni da wani namiji da'ya ne kawai zamu wakilci Najeriya, shi zai zama na b'angaren maza, ni kuma a b'angaren mata. Shi d'in d'an jihar Gombe ne." Cike da farin ciki na ce, "Alhamdulillahi Ya Allah! Kai amma wannan labari ya min da'di sosai wallahi. Har na ma rasa me zan yi dan murna. Allah ubangiji Ya taimaka Ya bada sa'a. Allah Ya baku ikon d'auko ma K'asarmu lamba ta farko a wannan gasa. Oh ni Murja! Wallahi jin abun nake tamkar a mafarki, wai 'yata da na haifa da cikina zata tafi wata K'asa gasar Al-Qur'ani mai girma, kuma wai 'Kasa baki d'aya zata wakilta. Ke alheri ce Amrah! Ke abar alfahari ce, wacce ko wace uwa zata so samun irinta. Ke abar koyi ce Amrah, wacce ko wace macen kirki zata so zama irinki. Allah Yana tare da ke Amrah, insha Allahu zai taimaka miki, zai baki nasara. Kuma na yi alk'awarin zan hana idanuwana bacci in kwana ina miki addu'ar samun nasara." "Ameen Umma. A lokacin da zancen nan ya tabbata, har da hawayen farin ciki na yi. D'alibaina kansu sun taya ni farin ciki. Daga masu kukan murna sai masu hawayen farin ciki. Matan auren da nake koya ma har da wacce ta rungume ni, wai ina ma iyayena zasu bata kyaur Malama Amrah, wallahi da ta gwada min k'auna fiye da yaran da ta haifa da cikinta." Ni d'in ma rungumarta na yi, idanuwana na kawo ruwa, ban sake ta ba, haka kuma a tsaye muke bamu zauna ba. A haka mallam ya tarar da mu, tun bai nemi bayanin dalilin halin da muke ciki ba, na hau zayyane masa komai, ina yi ina hawaye mai had'e da dariya. "Abin da ya dawo da ni gida ke nan, Murja. Ina wurin aiki na ji wani abokina yana saurarar radio, kamar an ce na d'aura kunnuwana a bisa bayanan, caraf kunnuwana suka jiye min sunan 'yata, a matsayin wacce zata wa'kilci K'asa baki d'aya, a musabak'ar da za a gudanar ta K'asa, a 'Kasar Sudan. Na kasa gasgata hakan, sai da na ji muryar Malaminsu da kanshi, yana mai nuna irin farin cikinsa. A k'arshe na ji muryar jakadan musaba'ka na jiha, yana nuna tashi murnar, da d'aya daga cikin d'aliban jiharsa ce zata wakilci 'Kasa ta b'angaren mata. Abun nan ya min dad'i kwarai da gaske. Na sake jinjina wa kaina, ke, da kuma 'yata. Tabbas samun 'ya kamar Amrah babbar sa'ar rayuwa ce. Amrah 'yata, ba zan ta'ba gajiyawa da shi miki albarka ba. Ba zan ta'ba daina miki fatan alkhairi ba." A haka wannan rana ta zame mana ranar farin ciki, farin cikin da na jima ban yi irinsa ba. Shi yasa ake so ka gode wa Allah a duk halin da kake ciki. Ka karb'i duk irin yanayin da mahaliccinka Ya yi ka. Kar ka butulce maSa saboda wata jarrabta da Ya yi maka, ko ba komai ka fi wani. Idan baka da lafiya, ka gode maSa, idan ka gode maSa, sai Ya baka ta wani fannin. Gashi dai duk wahalar da kika sha tsawon shekaru goma sha shida da watannin da na haife ki kike fama da ciwo, ciwo kuma mai matu'kar wahala, wanda babu wuya mutum zai iya kauce ma sharia, ya ji kamar shi ne aka fi tsana duk duniya. A haka muka jure, muka dage da addu'a, muka tsayanta Allah d'aya ne. A hakan da wahalar da kike, muka tarbiyyantar da ke, muka d'ora ki a bisa tafarkin kirki. A k'arshe mun ga ribar hakan, kin zama abar alfahari gare mu, malamanki, makarantarki, jiharki, da ma 'Kasarki baki d'aya." Annur kanshi sanda ya ji wannan labarin ya matuk'ar jin dad'i. Shi a gidajen talabijin ma ya ga sanarwar, kuma daga 'kasa aka mak'ala sunanta. Cikin lokaci k'ank'ane magana ta gama kewaye 'Kasa. Sunan Amrah ya shiga wurare da dama wanda bata ta'ba mafarkin zata je ba, sai ga sunanta ya je. Mutane da dama suke son ganinta, suke san sanin wai wacece wannan yarinyar mai tarin baiwa, wacce ta k'etare mutane da yawa, ta zama wa'kiliyar 'Kasarta? Ranar da zasu tafi, har Kano muka rakasu, ita da Malaminta. A iya inda zamu rabu, na kama hannuwanta duka biyun, na kalle ta cikin ido, na ce "Ina miki fatan alkhairi 'yata. Ba zan tab'a daina yi miki addu'a ba. Insha Allahu nasara tana tattare da ke. Allah Ya taimaka, Ya bada sa'a. Ki kula da kanki, Amrah." Wasu irin zafafan hawaye suka ringa kwarara daga idanuwana. Cikin kuka take wasa da hannuwana, cikin kuka take k'irk'iro murmushi, cikin kuka take fad'in, "Zan kula da kaina insha Allahu, Umma. Ki yafe min duk wani abu da na miki, b'oyayye da kuma bayyananne." Zare hannu guda na yi daga cikin nata, da shi na share hawayen da ina share sa ina dambe da wani, wanda ke shirin sake fitowa. "Baki ta'ba yi min komai ba Amrah. Banda alkhairi babu wani abu a tsakanina da ke. Idan ma akwaishi, na yafe miki." Na sakar mata murmushi. "Allah Ya 'kaddara saduwarmu, Umma." Ta fad'a had'e da zare hannuwanta daga nawa, ta rik'e na mahaifinta. Tun bata furta komai ba ya ce, "Baki ta'ba yi min komai ba 'yata. Idan ma akwai to na yafe miki. Ina mai neman gafararki, a bisa halin da muka jefa rayuwarki a ciki. Har yanzu na kasa yafe wa kaina. Har yanzu gani nake mu ne sila, mu muka jefa ki cikin wannan cutar. Ki yafe..." Bai rufe bakinsa ba ta saka tafukan hannunta ta dafe masa bakin nasa, "Bana son jin haka daga gare ka, Abbana. Komai na duniyar nan da zai samu mutum, to k'addararsa ce. Na sani, na kuma yarda cewa tawa k'addarar ke nan. Babu mai k'in d'aukar k'addara face butulu. Kar ka damu Abbana. Na yafe maka duniya da lahira. Na yafe maku kai da Ummana." Cikin hawaye take murmushi. Gaban Annur ta koma, wanda tun d'azu idonsa yake cikin nata. Murmushi ya 'kirk'iro mata, ba tare da ya furta komai ba. "Zan tafi Hammana. Ka yi min addu'ar samun nasara." "Nasara na tare da ke insha Allahu, Amrah. Allah Ya taimaka, Ya bada sa'ar abin da aka je yi." Lumshe idanuwanta ta yi, sannan ta sake bud'e su a kanshi. "Kar ka manta da ni, Hammana. Duk rintsi duk wuya, kar ka manta da Amrah. Ni ma ba zan tab'a mantawa da kai ba." Gyad'a mata kai ya yi, idanuwanshi cike da shauk'in soyayya, "Idan har zan iya mantawa da ke, to tabbas zan iya mantawa da kaina. Ke ce rayuwata, Amrah. Ke ce duk wani tunanina. Na so a ce tare zamu yi tafiyar nan, sai dai kuma Allah bai nufa ba. Ni ma tafiya ta taso min, zuwa K'asar Malaysia, ina tunanin sai kamar ana gobe zaku fara zan dawo. Amma duk da haka, rayuwata tana tare da ke, zuciyata tana tare da taki. Motsinki da komai naki yana tare da nawa. Ina matu'kar k'aunarki." Juyowa ta yi ta kalle mu, cikin jin kunya ta sunkuyar da kanta k'asa. Saurin d'auke kallonmu muka yi daga gare su. "Na gode k'warai Hammana. Na gode da sadaukar da rayuwarka da ka yi a kaina. Na gode da k'aunar da ka nuna min. Na gode da komai ma." Ta fashe da kuka sosai. "Ya isa haka to, please. Kin sani sarai, kin san yanda hawayenki yake da zafi a gare ni. Kin san yanda na tsani ganin zubar hawayenki. Kin san yanda rayuwata ta tsani ganin kin yi asarar hawayenki. Ki tafi, ga malaminki can yana ta jiranki." "To Hammana. Allah Ya k'addara saduwarmu." Ta tafi. Har ta isa iyakarmu da su bata daina waiwayenmu ba, bata daina hawaye ba. Baki d'aya jikina ya yi sanyi, na rasa dalili. Duk da ina son tafiyar tata, na san ci gaba ne a gare mu baki d'aya, amma a hakan ji nake kamar ta fasa tafiyar, kamar ta dawo gare mu. A haka muka kama hanyar parking lot. Muka shiga motar Annur, muka kama hanyar dawowa Katsina. _Tabbas soyayya gaskiya ce, wacce Allah ne yake d'aura ma mutum ita, ba tare da zuciyarsa ta shawarce shi ba. Abu mafi dad'i a soyayya, shi ne ka had'u da mai sonka tsakani da Allah. Ka had'u da mai k'aunarka, wanda zai sadaukar maka da rayuwarsa. Ina rok'on Allah Ya had'a mu da masoyanmu na gaske. Allah Ya aurar da mu ga masoyanmu na gaske._ pinky durling💗 *RAZ 2* [8/30, 3:36 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 2⃣0⃣ _Sa'kon gaisuwa ga tarin masoyan *AMRAH NAKE SO!* Kuna da yawa sosai, lissafo ku ba abu ne mai sau'ki ba. Sai dai duk inda kuke, ku sani cewa ana tare, ina yinku irin sosai d'in nan.😍_ *** Tun da muka shiga mota nake kuka, na rasa dalilin da yasa hankalina ya gaza kwanciya, damuwa da k'unci fal a cikin zuciyata. Mallam ne yake rarrashina, amma duk da haka na gagara yin shiru, ruwan hawaye basu daina kwaranya daga idanuwana ba. Bayan mun isa Hajiya Suhaila ta kira Annur a waya, har ya shaida mata cewa daga Kano muke, mun raka Amrah ne zasu tafi Sudan. Wayar tasa ya bani, ta nunar min da rashin jin da'dinta sosai, a bisa rashin yi mata bankwana da Amrah ta yi. Sam! Bata ji da'din hakan ba. Kuma ko kad'an tafiyar bata zata nan kusa ba ne, bata zata cikin satin ma zasu yi tafiyar ba. Ha'kuri kawai na bata sannan muka yi bankwana. Annur d'in ma ya bar gidan, wanda shi kanshi idan ka kalle shi zaka tabbatar yana cike da damuwa. Ko da dare ya yi haka bacci ya gagara d'aukata, na ringa juyi, damuwa ta gama mamaye kaf ilahirin zuciyata. Yau d'in nan Amrah ta tafi, amma ji nake kamar ta yi sati bata nan. Rayuwarta nake tausayi, mafi rinjaye a k'aunar da nake mata, ta ta'allak'a ne da tausayinta da nake, tausayin rayuwarta, tausayin yawan ciwukanta. Tuno bankwanan da muka yi da ita kawai nake, ina tuna murmushin da take yi mai had'e da ruwan hawaye, da kuma yanda ta ringa wasa da hannuwa. Wasa ba wasa ba, yanda na ga rana haka na ga dare. Jin kiraye kirayen sallar asuba na yi, wanda ko kad'an ban zata daren har ya kai haka ba. Bayan gari ya waye ne Mallam ya duba wayarsa, ya ci karo da text da ta masa cewa sun sauka lafiya, yanzu haka suna masaukinsu. Hamdala na yi a lokacin da ya bani labari. Ban san sanda na saki wani murmushi ba. Baki d'aya zuciyata na ji ta wanke, duk k'uncin da nake ciki babu shi. "To Alhamdulillah! Sauka lafiyan dama ake buri. Zan kira ta anjima insha Allahu, gudun kar na shiga lokacinta yanzu." Mallam ya furta shi d'in kanshi farin ciki lullub'e da fuskarsa. A kai a kai muka ringa gaisawa da ita a waya, duk sanda zamu yi waya kuwa zan shi mata albarka, zan mata fatan alkhairi. Haka ma mahaifinta. Ana gobe zasu fara musabak'ar Annur ya dawo, ya zo gaishe mu ne nake masa tad'inta, ta ce min za a nuna musaba'kar a tashoshi da dama, ciki kuwa har da sunnah tv, ni kuma gashi bamu da kayan kallo. "Zan zo har nan mu kalla a waya' insha Allahu. Ai ina nan sai ranar Sunday zan tafi. Na san zasu saka live a internet." Annur ya fad'a yana min murmushi. Cike da jin dad'i na ce, "Yauwa to, aiko da na ji dad'i sosai. Allah Ya nuna mana goben lafiya." "Ameen, Umma. Bari na tafi. Idan Abba ya dawo a gaishe shi." "Zai ji 'kwarai. A gaishe da Hajiya Suhailar. Ka mata albishir, ta tara gobe ta kalli 'yar tata." "Zan fad'a mata, Umma." Ya tafi. Washe gari kuwa kusan k'arfe goma sai gashi ya zo. Malam dama ya ce ba zai fita aiki ba har sai sanda muka gama kallon musabak'ar, ko kwana nawa za a d'auka ana yinta kuwa. Ko da ya kunna mana muna kallo, da 'Kasar Egypt aka fara. Namijin ya fara sannan macen ma ta yi. A haka aka ringa yi, ba laifi karatu ya yi sosai, sai dai abin da ba za a rasa ba. Har aka gama ta ranar ba a kira Najeriya ba. Haka yasa Annur ya ce zai tafi, gobe insha Allahu kafin a fara zai dawo, sai mu ci gaba da kallo. Hakan ce kuwa ta kasance. Abun mamaki har a ranar ma ba a kira K'asarmu ba. Sai ranar k'arshe, wacce kuma ita ce Annur zai tafi, amma a haka ya kashe tafiyar ranar, ya mayar da ita ranar litinin, dan kawai ya faranta mana rai. Najeriya ce ta k'arshe, sai da namijin ya yi, kafin aka kira Amrah don ta yi. Ban san sanda na mik'e ba, ganin 'yata ta doso mazaunin masu musabak'ar, cike da natsuwarta. Wani kwali ne mai kyau aka mik'o mata, wanda a cikinsa ne ta d'auko takarda guda d'aya, ta mik'a ta ga wani wanda aka tanadar domin mik'awar kawai, shi kuma ya isar da ita ga alk'alan musabak'a. Jan farko aka fara yi mata, a cikin suratul Bak'arah. Haka ta ringa zayyano karatunta babu kuskure, ko jar danja d'aya ba a mata ba har aka haska mata tsanwar danja, wadda ke nunar da zata dakata daga nan. Wani jan aka mata, cikin suratul Yunus, nan ma dai haka ta ringa karatu babu kuskure ko kad'an. Daga nan sai suratul Noor. Murmushi ta saki a sanda aka jawo mata ayar farko, tana jin da'din surar, tana matuk'ar son surar, gata kuma sunan sahibinta ne. Tun asali ta sha wahalar surar ne, sanda take hardarta har kuka ta ringa yi, saboda matuk'ar wahalar ayoyin cikinta. Amma daga sanda ta iya, sai k'aunarta da take yi. Kamar mai bada labari haka ta ringa karatu, babu kuskure bare tangard'a a karatunta. Cikin ja na hud'u ne aka ja mata suratul-Yaseen. A nan kam ta dad'e tana karatun, saboda wannan shi ne ja na k'arshe da za a mata, kuma dama a kan jima kafin a dakatar da mutum. To gashi kuma dama ita ce mutum ta k'arshe a musaba'kar baki d'aya. A daidai "kun fa yakun." Ta dire, tun bata fad'i ayar k'arshen ba ta kwanta a saman bencin, saboda irin kujerun nan ne masu had'e da teburinsu, amma na k'arshe, masu k'irar gidan sarauta. Tana duk'ewa kuma da alama dama ta kai k'arshe, tsanwar danja aka haska mata, wacce ke nunar da ta gama karatunta ke nan. Tun da ta duk'e bata taso ba, da dama an yi tunanin ko dan karatun da ta yi ne, saboda da wasu idan suna karatu kuka suke yi. Mu d'in ma kanmu haka muka yi zato. Sai dai kuma abun mamaki, ta fi k'arfin minti goma a haka, ko motsi kanshi ya gagare ta. Cike da mamaki aka nuno yanda alk'alan suke kallon kallo wa junansu, suna neman sanin dalilin duk'iyar tata. Umurni suka yi ga d'aya daga cikin mata securities da suke gadin b'angaren da mata suke, kan ta zo ta ga ko kuka ya ci k'arfinta ne ya sa ta kasa ta shi. Isowar kuwa ta yi inda take, kuma har a lokacin ba a daina d'aukar video ba. Muna kallon komai da yake faruwa a kan idanuwanmu. Sai dai mun gagara furta komai a tsakanin mu duka ukun. Tashin hankali, wanda ba a saka masa rana. Matar na d'an jijjiga Amrah kad'an, sai ta rikito daga bisa kujerar ta fad'o k'asa. Take Annur ya sake wayar tasa k'asa a rikice, har sai da ta yi rugu rugu. Ya dafe gefen da zuciyarsa take, idanuwansa suka kawo ruwa, jikinshi ya hau rawa baki d'aya. A yanda muka ji labarin faruwar abun, wai daga sanda suka ga ta fad'o d'in, hankalin mutane da dama dake wurin ya tashi, take aka yi waya aka kawo ambulance, domin a kai ta asibiti. Babu jimawa kuwa sai ga motar ta iso, tun wanda suka d'auke ta d'in, suka tabbatar cewa gawa ce, bata raye. Amma gudun akasin haka, yasa suka yi shiru, tare da malaminta, da sauran jakadan Najeriya suka tafi asibiti. Sai dai suna zuwa, likita ya tabbatar masu cewa bata raye, ta rasu. Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Mun shiga tsananin tashin hankali Maryama. Ba zan ta'ba iya kwatanta miki adadin tashin hankalin da muka shiga ba. Amrah ta rasu, Amrah bata raye, Amrah ta mutu ta bar mu. Shi ke nan mun rasa ta, shi ke nan mun rasa Amrah, ba zata tab'a dawowa gare mu ba. Malaminta aka sa ya kira ya sanar mana, shi d'in kanshi cikin kuka muke waya da shi, cikin kuka yake sanar da mu abin da ya faru. A can aka binne gawarta, gudun kar a d'auki dogon lokaci kafin a iso da ita Najeriya. Har da hoton gawar aka d'auka aka gwada a gidajen talabijin da dama, ana sanar da rasuwar baiwar Allah'r da sai da ta gama musaba'karta, a bisa teburin Allah Ya kar'bi rayuwarta. Duk wani mai imani sai da ya girgiza da wannan al'amari mai matuk'ar d'aure kai. Wadda dubban al'umma sun kalli komai da ya faru. Sun saurari daddad'an karatunta. Sun ga yanda ta rikito 'kasa, har lokacin da aka d'auke ta. A yadda sanarwar ta zo, Amrah ce ta zo d'aya a wannan musabak'ar, ita ce wacce ta fi kowa maki, ba wai a mata kad'ai ba, har ma da mazan baki d'aya. Duk wata kyauta tata zasu damk'a ta ga malaminta, da kuma jakadan Najeriya, su isar da ita ga magadanta. Ko da Malamin nata ya sanar mana a waya, cike da tashin hankali Mallam ya ce masa kar ma ya karb'o, a mata sada'katul jariya kawai da su. Mu kam mun yafe. Kujerar Makkar da aka bata ma, mun sadaukar da ita ga malaminta, ya je ya yi aiki, ya mata addu'a. Saboda a halin tashin hankalin da muke ciki, bana jin zan iya amfani da duk wani abu wanda ya shafe ta. Annur kuwa dama tun daga lokacin da labarin rasuwarta ya riskemu ya sume, bai sake farfad'owa ba, har sai da ya yi kwana biyar a haka. Ko da ya farfad'o da sunan Amrah ya tashi, yana fad'in, "Dan Allah ku ce min mafarki nake, ku tasar da ni daga wannan mummunan mafarkin da nake yi. Wallahi ba zan iya rayuwa ba tare da ita ba. Amrah ce wani 'bare na zuciyata, ita ce tunanina baki d'aya." Kuka yake sosai, wanda dole duk na kusa da shi sai ya tausaya masa. Rasuwar Amrah na d'aya daga cikin rasuwar da ta girgiza al'ummar Najeriya. Ta shiga record na Najeriya. Wai ashe bankwana muka yi da Amrah a lokacin da zata tafi. Ashe ganin 'karshe na mata. Ashe ba zan sake ganin y'ata ba. Ashe mutuwa zata mana yankan k'auna. Ranar da Annur ya farfa'do ne ya tilasta ma Hajiya Suhaila cewa zai zo inda muke, akwai maganar da yake son yi da mu. Duk da halin da yake ciki, a haka suka zo, su duka jikinsu sanyaye. Kallo d'aya na ma Annur hankalina ya tashi, na sake tuno da y'ata, nake ganin kamar tafiya ce ta yi, zata dawo gare ni. Shi kanshi Annur d'in abun tausayi ne. Cikin lokaci 'kank'ani ya gama zubewa, ya koma kamar zautacce. Cikin kuka na masu iso, Hajiya Suhaila ce ta zauna bisa tabarmar, Annur kuwa k'asa ya rashe, yana wani irin kuka mai tsuma zuciya. Yana gyad'a kanshi, da alama magana yake son yi amma ta gagara fitowa. "Sannunku da zuwa Hajiya." Na furta cike da k'arfin hali, muryata da ta gama disashewa da k'yar ta fito, har ake jin abun da na fad'a. "Ya kamata ku daina kukan nan haka nan. Bai kamata ku ma Amrah kuka ba, sai dai kukan sabo kawai. Amma irin mutuwar da Amrah ta yi, mutuwa ce wadda kowa zai yi fatan ya yi irinta. Amrah ta yi kyakkyawan k'arshe, kuma dama an ce mutum zai tashi a kan abin da ya mutu yana aikatawa, ke nan Amrah zata tashi tana karatun littafi mai tsarki. Ga Annur nan, shi ya takura lallai sai ya zo, akwai maganar da yake son ya yi da ku." Ta k'arisa maganar tana mai gya'da kanta. "Umma..." ya fad'a cikin rawar murya, yana mai k'ok'arin had'iyar k'wallarsa. "Umma shi ke nan...shi ke nan na rasa ta. Na rasa Amrah har abada, ta tafi ta barni, bayan kuma alk'awarin da muka ma junanmu na rayuwa tare. Amrah ta tafi ta barni..." Ya sake fashewa da wani kukan. Ni ma kukan nake sosai, na du'kar da kaina ka'sa, ina k'ara tuna rayuwar Amrah, rayuwa mai cike da abubuwan koyi, rayuwa mai tsananin ban mamaki. "Umma...bana jin zan ci gaba da rayuwa a doron k'asar nan. Bana jin rayuwata zata yi kyau matuk'ar babu Amrah a cikinta." Kuka riris yake, kamar jinjirin da ya jima bai ci abinci ba. Shesshek'a yake sosai, idanuwanshi na nunar da tsantsar damuwar da yake cikinta. _Dan mutum yana fama da wata cuta, ba lallai ba ne a ce ita zata zama silar mutuwarsa. Kar dan kana ciwo, ka ringa tunanin lallai lokacin tafiyarka ya kusa. Ita cuta ba mutuwa ba ce. So da yawa mai lafiyar ma yana mutuwa ya bar wanda yake ciwo. Kamar yanda muka gani a rayuwar Amrah. Mun ga yanda ta kasance mai ciwo, tun tana 'yar shekara d'aya a duniya, har ta gama mallakar hankalinta kullum cikin ciwo take. Mun ga yanda cutar sickler bata zama ajalin Amrah ba. Mun ga yanda ta mutu babu ciwo, sai dai gawarta kawai. Ikon Allah ke nan._ _Ya Allah! Ka sa mu yi kyakkyawan 'karshe. Allah ka sa mu cika da imani. Allah Ya ji k'an magabantanmu. Wanda suka rasa iyaye, Alllah Ya ji k'ansu da rahama. Wanda suka rasa makusanta, ko kuma wasu malamansu, Allah Ya had'a mu a darussalam. _*I was crying when I was typing this chapter. Ba wai kukan littafin ba, a'a, kukan rayuwa kawai, kukan mutuwa, wacce dole zata zo mana komin daren dad'ewa. Ni, ke, kai, ku dole wata rana zata d'auke mu. Me muka tanadar mata? Idan yanzu Allah Ya zare ranmu, me muka shirya na had'uwa da Mahaliccinmu?*_ wattpadians, comment on each line. Ko da ban samu damar baku amsa ba, kuna raina. Thanks. Pinky durling💗 RAZ 2 [8/30, 3:37 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 2⃣1⃣ _*AMRAH NAKE SO* the book, everywhere you go. I don't even know what to say but Thank You very much. Am very very sorry for the last chapter, cuz, every soul shall taste death kaman yanda Allah mad'aukakin sarki Ya fad'a. We're all waiting for it, now, tomorrow, next tomorrow or even next year. Allah kad'ai Ya bar ma kansa sani. Fatanmu dai, Allah Ya sa mu cika da imani._ *** Shiru kake ji a kaf ilahirin gidan, in banda shesshek'ar kukan Annur babu abin da ke fita. Kwana biyar ke nan da rasuwar Amrah, amma kamar yau aka yi ta, kullum d'anya shar take dawo mana. Nannauyar ajiyar zuciya Hajiya Suhaila ta sauke, cikin muryar da ke nunar da tausayi ta ce, "Ka fad'i abin da kake son fad'i, Annur. Ka ga baka da lafiya, mu samu mu koma ka kwanta, Islam ta duba lafiyar zuciyarka. Dan wannan halin da kake ciki, babu wuya zuciyarka ta samu matsala. Though bama fatan haka." "Gaskiya fa." Na furta had'e da share k'wallar da ta sake fito min. "Amrah ta riga da ta tafi, duk wata damuwa ko kuka namu, ba zasu tab'a dawo da ita ba. Ta tafiya inda ni, da ku duka sai mun je, komin daren dad'ewa. Addu'armu kawai take da buk'ata, ita ce kawai zata nunar da zallar soyayyar da muke mata. Ta nan kawai zamu saka mata da kyawawan halayen da ta kasance tana da su sanda tana raye." Kyarma yake sosai, zuciyarsa na tafarfasa da kalamaina. Na yi da nufin ya yi shiru, amma sai k'arfafa kukan nasa ma da ya yi. Da k'yar cikin wata murya ya ce, "Ya zan yi rayuwa ba tare da Amrah ba? Ya zan ci gaba da numfashi a doron k'asa ba tare da baiwar Allah'r da aka gina rayuwarmu domin mu so junanmu ba? Ta yaya? Ta ya zan iya Umma? Momy ku fad'a min, ya zan yi da rayuwata? Wallahi *Amrah nake so,* ita kad'ai. Amrah nake k'auna, bata da kishiya..." Ya sake dafe zuciyarsa, yana wani irin kuka, wanda ban tab'a jin irinsa ba. Ba wani sauti ne da shi ba, sai dai ya bayyanar da yanda yake fitowa kai tsaye daga zuciyarsa. "...Baki d'aya rayuwata na sadaukar da ita ne gare ta. Hankalina, tunanina duka tare suke da nata. Jini da jijiyoyin jikina duka tare suke gudanya da na Amrah." Yana kaiwa nan ya runtse idanuwansa, yana mai k'ok'arin danne sabbin hawayen da ke fitowa, "Mutuwa dan Allah ki zo ki d'auke ni, ki zo ki tafi da Annur, ki kaishi inda Amrah take..." Saurin dakatar da shi na yi, cikin kuka na ce, "Kar ka yi sab'o, Annur. Dukkanmu nan ko ba dad'e ko ba jima zamu tafi, zamu je inda Amrah ta je. Dukkan mai rai mamaci ne, haka Allah mad'aukakin sarki ya fad'a a cikin littafinsa. Baki d'ayanmu jiran lokacinmu muke yi. Ita d'in kanta Amrah ba wai gaggawar tafiya ta yi ba, a'a, iyakacin lokacin da ta d'ibo wa kanta ke nan. Dan haka mu sakawa zuciyoyinmu salama, mu mik'a lamurranmu ga Allah, mu ma Amrah addu'a. Ka ci gaba da addu'a ma kanka kai ma, insha Allahu, Allah zai had'a ka da kamar Amrah, wacce zata soka, kaima kuma zaka so ta kamar Amrah..." "Ba dai a duniyar nan ba, Ummah. Bana jin akwai mai irin halaye da d'abi'u irin na Amrah. Ko da ma akwai, bata dame ni ba. Ba ma sai idan zan iya ci gaba da rayuwar ba, bare har na had'u da wacce kike fad'i? Mutanen da komai nasu yake a had'e, Umma, kina tunanin lokaci guda zasu iya rabuwa? Bana tunanin haka." Ya dakata daga nan, yana taunar lab'bansa. Da k'yar ya iya ci gaba, "Maganar da nake so na miki, dama alfarma nake nema a gare ki, Umma." "Ina saurarenka." Na furta cike da tausayinsa. "Baki d'aya kayan aurenta, da wanda kuka siya, da wanda aka kawo daga gidanmu, nake so ku had'a a gina mata Masallaci babba, ko kuma wata Islamiyya, a matsayin sadak'atul-jariyah. Ina son lada ta ci gaba da kai ma Amrah, ta samu rabo mai k'wari a wurin mahaliccinta." Wani sabon hawayen ya sake fito min, da k'yar na k'irk'iro murmushi na ce, "Insha Allahu haka za a yi, Annur. Ko jiya da dare mun fara magana da Mallam, cewa nan da kamar sati d'aya zamu had'a komai da kuka kawo a mayar maku, saboda mu dai nan babu abin da zamu yi da su wallahi. Ganinsu da nake ma sake shiga tashin hankali kawai nake. Ina tuna mai su, wacce babu wanda ya tab'a tunanin ba zata amfane su ba." A wannan ga'bar kam, Hajiya Suhaila kanta kuka ya kufce mata, wanda da alama tun zuwansu yake son fitowa, take yak'i da shi domin ya koma. "Haba Maman Amrah. Ke ma kanki kin san ba zamu tab'a kar'bar kayan nan ba. Yanda suka fito daga gidanmu, suka zo nan gidan da nufin na Amrah ne, to natan ne. Duk ma yanda zaku yi da su dai sun zama na magadanta. Maganar da Annur ya yi mai kyau ce. A mata sadak'atul-jariyah kawai." Mallam da ya shigo daidai nan ya jinjina kansa, samun wuri ya yi ya zauna a kusa da Annur, ya dafa kafad'arsa cike da bashi k'warin guiwa, murmushi lullub'e a saman fuskarsa. "Annur, d'ana." Ya furta idonsa cikin nashi. "Kai fa namiji ne ba mace ba. Ya zaka ringa yin abubuwa kamar dai mace? Ko ka manta dama rayuwar tamu dukanta aro ce, watan wata rana sai wanda Ya bamu aron Ya karb'e abarSa? Ba zan hana ka yin kuka ba, sai dai kuma a ganina sam! Amrah bata cancanci a mata kuka ba. Yarinyar da duk wanda ya bud'e bakinsa shaidar kirki zai bata. Duk wanda ya san Amrah ya santa da halayen kirki. Natsuwa, girmama mutane, karamci, kamun kai, duka halayenta ne. Ka ga kuwa ai ba abar a mata kuka ba ce. Tun daga sanda aka yi sanarwar rasuwarta, yau kwana biyar ke nan, babu ranar da ba a fad'in rasuwarta a gidajen radio, babu ranar da ba a d'ora karatunta a gidajen talabijin. Kullum da mutanen da suke kirana a waya, da wanda suke zuwa har gida, ba wai dan sun sanmu ko ita Amrah'n ba, sai dan labarin rasuwarta da ya kewaye al'umma. Dan Allah Annur ka cire damuwa daga zuciyarka. Kar ka bari damuwa ta illata maka zuciya, kai d'in ma mu rasaka kamar yanda muka rasa Amrah, ba zamu so hakan ba." Sai a nan Mallam ya dakata, ya saki kafad'ar Annur d'in, yana masa murmushi mai tabbatar da maganganun da ya fad'a masa. Hajiya Suhaila ta ce, "Ni kaina abin da na nunar masa ke nan. Allah fa baYa barin wani dan wani ya ji dad'i. Amrah kuma lokacin tafiyarta ne ya yi, kuma dole zata tafi ko ba dad'e ko ba jima, ko da ba yanzu ba." "Haka ne, Hajiya. Akwai damuwa kam, amma dole sai an daure." "Yanzu Annur ka tashi ku je, a duba mana lafiyarka. Dan Allah." Na fad'a bayan na sauke ajiyar zuciya. Tashi kuwa ya yi jiki babu k'wari, tangal tangal ya yi kamar zai fad'i, sai da Mallam ya hanzarta ri'ke shi da iya k'arfinsa. Har mota ya kai shi ya zaunar, sannan ya ma Hajiya Suhaila bankwana ya dawo gida. A lokacin da ya dawo, ya same ni ni d'in ma na dasa wani sabon kukan, tausayin Annur da kuma rayuwar da zai fad'a kawai nake. Ranar da Amrah ta cika sati da rasuwa Mallam da kanshi ya fidda komai nata, aka sadakar da wasu, wasu kuma aka had'a shi da wata mata wacce ke siyan komai na aure, tun daga kayan d'aki, zuwa kayan lefe da komai ma. Siyan wulak'anci ta ma kayan, amma a haka sai da aka had'a kud'i kusan miliyan d'aya da dubu d'ari biyu, dan inda siyayyar mutunci ta masu ma, sai sun kai miliyan uku. Ko lefenta kad'ai ya fi miliyan da rabi. Da wannan kud'in ne aka gina wannan Islamiyyar, da su ne aka saka duk wasu kujerun da suke ciki. Aka saka ma islamiyyar suna *MADRASATUL AMRAH BNT ABDALLAH.* Kud'in da yara ke biya duk wata da su ne ake biyan Malaman albashi daga farko, amma daga sanda Islamiyyar ta bunk'asa sosai, gwamnati ta d'auki nauyin albashin malaman, kuma aka yi sa'a hakan ya d'ore. Kud'in makarantar yara kuma duk wata ake kaiwa gidan marayu, da nufin Allah Ya kai ladar ma Amrah. Annur kuma tun daga ranar da suka yi wannan zuwan shi da Hajiya Suhaila, ban kuma jin labarinsa ba. Ranar da abun ya dame ni, na yanke hukuncin zuwa har gidansu don jin halin da yake ciki. Tare da Mallam muka kama hanyar gidan nasu, ko da muka isa, kai tsaye aka mana iso har d'akin Hajiya Suhaila. Ko da ganinmu kuka ta fasa da 'karfi, wanda har sai da ya razanar da ni. Kukan nata ba na wasa ba ne, duk wani mai zuciyar imani dole zai tausaya ma Hajiya Suhaila, ganin Babbar mace na kuka wiwi, kamar k'aramar yarinya. Da hanzari na isa inda take, na dage idanuwana da ruwan hawaye suka fara fitowa, na zauna k'asan kujerar da take. "Hajiya Lafiya?" Na furta cikin k'arfin hali. "Babu lafiya, Maman Amrah." Sanda ta fad'i maganar ras! Na ji gabana ya fad'i, jikina ya d'auki rawa, lab'bana sai k'yarma suke, ina son yin magana amma na kasa. "Annur ya haukace, Maman Amrah. Ya haukace tuk'uru hauka yake." Mik'ewa na yi tsaye ina zare idanuwa, da mamaki na ce, "Hauka, Hajiya Suhaila?" "Hauka kuwa. Tun ranar da muka baro gidanku na rasa gane ma kansa. Sai sabbatu yake yana fad'in *"AMRAH NAKE SO"* ya yi dariya, sai kuma ya fashe da kuka a k'arshe. Gudu yake tik'awa iya k'arfinsa wai zai je inda Amrah take, sai an kamo. Abun kamar wasa, yanzu haka yana wancan d'akin an d'aure shi. Saboda idan aka sake shi, ko an rufe d'akin ya ringa bubbuga shi iya k'arfinsa ke nan. Ya nemi b'ab'balla komai dake cikin d'akin. 'Yar uwarsa ce ke masa allura, kafin mu ga gudun ruwan abun." Ta k'arisa maganar da sadda kanta, tana kuka sosai. Ni d'in kaina kukan nake, jin shi nake tamkar d'an da na haifa da cikina, saboda duk wata damuwa ta Annur tamkar tawa ce. Yadda Annur ya kula da Amrah sanda tana raye, ya so mu, ya kula da rayuwarmu baki d'aya. Dole in damu da shi, in damu da halin da yake ciki. Mun nemi mu ganshi ta raka mu har bakin d'akin, sai dai ta taga muka hango shi kwance yana bacci, wai Islam ce ta masa allurar bacci. A haka muka dawo gida jiki sab'ule, babu mai furta komai a tsakaninmu ni da Mallam. _Ba a gama halittar mutum har sai sanda ya kwanta damarsa. Ka san farkonka, haihuwarka aka yi. Ka san k'arshenka, mutuwa zaka yi. Amma baka san tsakiyarka ba, baka san me zai same ka ba, baka san wace gwagwarmaya zaka fad'a ba. Wasu su zama nak'asassu, bayan lafiya lau aka haife su. Wasu su haukace, bayan ba a haife su da hauka ba. Addu'a kawai zamu yi, Allah Ya kare mu, Ya kare zuri'armu, Ya kare al'ummar musulmai baki d'aya_. Dont forget to vote and comment. I love you irin totally din nan. Pinky durling💗 *RAZ 2* [8/30, 3:37 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 2⃣2⃣ Tun daga ranar da muka dubo Annur hankalina ya sake tashi, ga kewar Amrah, wadda a kullum take dawo min sabuwa dal. Ga kuma rashin lafiyar Annur, wadda ta gama tasar min da hankali, ta k'ara min imani, na k'ara tabbatar da cewa lallai mai rai ba a bakin komai yake ba. Ikon Allah ya fi gaban mamaki. Babu k'arfi babu dabara face a wurin Allah ma'daukakin sarki! Shi yake juya al'amari a duk sanda Ya ga dama. Shi ne mai d'ora ciwo, Shi kuma yake bada waraka. Duk dukiyar Alhaji Iqra Al-Hussain ta kasa sama ma d'ansa lafiya. Gashi dai babban pharmacist wanda yake sananne ne, amma ya kasa gano maganin da zai warkar da d'anshi. Ga kuma Dr. Islam, wacce take k'anwa ce ga Annur, kuma likita amma likitancinta bai tasiri ba. Yawace yawace har wasu k'asashe aka je, daga 'karshe aka had'a su da wani babban likita, wanda b'angaren k'walwa kawai yake da ilimi, wato Dr. Aqaq Saifullah. Dr. Aqaq ya amsa sunansa wurin likitancin abin da ya samu k'wak'walwa (wanda suka karanta labarin HZ ko kuma MH zasu san shi) yana da wuya ya yi aiki ba a yi nasara ba, amma a gefen Annur kam babu ci gaba, sai ma ci baya da ake samu. Kusan wata hud'u ke nan da rasuwar Amrah, amma zancen rasuwarta ya 'ki ficewa daga bakin al'umma. Duk ta inda ka gitta zancen rasuwarta ake. Bayan wasu lokuta na samu labarin Annur ya warke sosai, sai dai kuma an samu matsala! Ya zama rik'ak'ken mashayi, mazinaci, mai munanan d'abi'u. Abun haushi da takaici, har gidan su Annur na je domin mu gaisa, saboda tun da ya warke bai tab'a zuwa inda muke ba. Amma wai kai tsaye yaron nan ya wulak'anta ni. "Ke Malama ki shafa min lafiya, ni bakya gabana." Kawai ya ce da ni, da wani bak'in gilashi a fuskarsa, ba tare da ya zare shi ba. Salati na yi a cikin zuciyata, 'Wata 'kila dai tab'in k'walwar nan bai sake shi ba.' Na furta a cikin zuciyata. Sanda Hajiya Suhaila ta zo ta same mu a haka, take bani ha'kuri kan cewa wai tun sanda ya warke ya koma haka. Baki d'aya rayuwarsa ta canza, bashi da aiki sai wula'kanci, su kansu ba wani girmama su yake yi sosai ba. Kuma babbar matsalar mahaifinsa ya d'aure masa gindi, baya bari ko kad'an a fa'di laifinsa. Cike da mamaki haka na bar gidan, zuciyata bata daina mamakin abin da ya faru ba. A daidai k'ofar fita na sake cin karo da shi yana k'ok'arin fita hannunshi rik'e da makullin mota, "Am...dan Allah, kar na sake ganinki a gidan nan. Ala'kar ai ta zo k'arshe tun da dai wacce ta had'a mun ta rasu. Kowa ya tsaya inda Allah Ya ajje sa. Idan ba haka ba kuma, bani da wasa..." ya zare gilashin ya kallen ido cikin ido, had'e da sakin wani mummunan murmushi. Ban san lokacin da na ji hawaye ba. Nake tunanin wasu lokuta da suka gabata. Nake ji ina ma dai a ce mafarki nake ba gaske ba. Da hawaye na bar gidan, har na isa gida zuciyata bata daina jimamin abin da ya faru ba. Mamakin kalaman da d'an da na isa haifa da cikina ya fad'a min kawai nake. A zuciyata har sak'e sak'e nake, wai anya dama da gaske Annur yana son Amrah? Idan har yana sonta, rashinta ba zai sa ya min haka ba. Sai dai kuma wani shashen na zuciyata yake gasgata min da soyayyar da Annur ya ma Amrah ta gaskiya ce. Nake tuna yanda ya sadaukar mata da lokacinsa tun yarintarsa har ya fara mallakar hankalinsa. Nake tuna rabawar da aka masu sanda zai tafi Cyprus. Ga kuma halin da ya shiga lokacin da ta rasu. To me yake faruwa? 'Hauka ne bai sake sa ba.' Wata zuciyar ta bani amsa. A haka na isa gida, baki d'aya jikina a mace yake, na rasa me ke min dad'i. Tun daga wannan ranar ban sake zuwa gidan su Annur ba, shi d'in ma ko hanya bata tab'a kawo sa nan ba. Hajiya Suhaila ce ma wani lokaci takan zo mu gaisa, ta kawo mana abubuwan buk'ata. Tun daga rasuwar Amrah, yau shekara biyu da watanni ke nan, duk bayan wata uku sai gwamnati ta bamu naira dubu d'ari biyu kyauta, kawai saboda abin da ya faru. Islamiyya kuma ta ci gaba da bunk'asa, da dama malaman waccan Islamiyyar ta su Amrah sun dawo wannan, sun sadaukar da lokutansu, duk saboda abin da ya faru ga Amrah. Wannan shi ne labarin Amrah. Yarinya ta gari, yarinya abar alfahari kuma abar koyi. Mun rasa Amrah, mun rabu da ita, Amrah ta rasu a wurin gasar karatun Al-Qur'ani mai girma." Ta k'arisa maganar da kuka sosai, tana jin mutuwar Amrah ta dawo mata d'anya shakaf, tana jin tausayin muguwar rayuwar da Annur ya jefa kansa. Kuka sosai Maryama ke yi, idanuwanta sun yi luhu luhu, shesshek'a take kamar wacce aka ma dukan tsiya. Cikin kukan ya ce, "Allah sarki! Allah sarki Amrah. Lallai kuwa na tabbata...na tabbata cewa rayuwarki babu komai a cikinta face tausayi, da kuma ababen koyi. Wayyo Allah, Amrah..." ta kuma fashewa da kuka. "Na ta'ba jin rasuwarta tun sanda nake makaranta, a boarding School, sai dai ko kad'an ban san ita ba ce, saboda ban san sunan waccan d'in ba. Kawai dai na ji an ce wata yarinya ta rasu a wurin musaba'ka. Ashe Amrah'n da nake Islamiyyarta ce." Ta dire maganar had'e da jan numfashi da k'arfi. "Amma Umma bakya tunanin ko k'walwar Annur ce bata gama warkewa ba, yasa ya miki haka?" "Maryama, lokacin da yake cikin haukan tuk'uru fa idan ya ganmu har k'ok'arin 'kwace kansa yake wai zai zo inda nake, zai zo na kai shi inda Amrarshi take. Shi yasa abun ya dad'a bani mamaki. Na kasa jin haushinsa a zuciyata, duk kuwa da irin wula'kancin da ya min." Gya'da kai Maryama ta yi, cikin kuka ta ce, "Na miki alk'awari zan ci gaba da kula da ke , Umma. Zan zama abar alfahari a gare ki. Zan zame miki tamkar Amrarki da kika rasa shekaru biyu da suka gabata." Rungumar juna suka yi, ko wace cikinsu tana kuka. Sosai Umma ta ji dad'in abin da Maryama ta fad'a, tana jin a jikinta ta yi 'ya. "Insha Allahu zan kawo Mamana har nan ku gaisa, da kuma k'anina Muhammad. Zan kuma kai ki gidanmu dan ki gani, sai a ci gaba da zumunci sosai." Umma ta ce, "Allah ya tabbatar da hakan, Maryama. Ki ce dai Amrah ta tafi, wata Amrar ta dawo." Ta saki murmushi mai had'e da hawaye. "Insha Allahu kuwa, Umma. Ni ma mu ne manya a Islamiyyarmu, mu za a fara yi ma walimar sauka nan da 'yan makwanni. Insha Allahu zan k'ara dagewa, zan jure, zan yi karatu sosai, saboda zan so zama kamar Amrah. Zan so na zama abar koyi, kamar yanda Amrah ta zama abar koyi. Zan so na yi rayuwa mai kyau, kamar yanda rayuwar Amrah ta kasance, ta bar bayanta da kyau." Mallam ne ya shigo da sallama a bakinsa, Umma ta amsa had'e da mik'ewa ta karb'i ledar hannunsa. "Barka da dawowa, Abba." Maryama ta furta cikin girmamawa. "To, Marayama ce? Sannu kin ji. Kin zo ke nan." Da fara'a ta ce, "Na zo, Abba. Har ma Umma ta gama bani labarin rayuwar Amrah." Gyad"a kai Mallam ya yi cike da tausayi ya ce, "To buri ya cika, Maryama. Yau dai kin ji abun da kika jima kina son ji daga bakin Mallam Sallau. Kin san wacece Amrah, kin ji irin gwagwarmayar da ta sha a rayuwarta. Yanzu abin da ya yi saura kawai sai ki yi koyi da Amrah, ki zama mai irin zuciyarta, wacce babu komai a cikinta face kyakkyawan kud'uri. Ba wai dan Amrah tana 'yata ba, amma na yi imani da Allah irinta basu da yawa a wannan zamanin. Samun yarinya budurwa, mai shekaru kamar na Amrah, da tsarkakakkiyar zuciyarta zai yi wahaka. Ina ro'kon Allah da Ya ji 'kan Amrah. Allah Ya mata rahama, Ya haskaka makwancinta. Maryama kin ji yanda rayuwa bata da tabbas ko? Kin ji yanda mutum yake mutuwa ba tare da ciwo ba ko? Kin ji babban kuskuren da muka tafka kafin mu yi aure ko? Rashin awon genotype babbar damuwa ce, savoda baka san hakin da zaka jefa yaranka ba a gaba. Gashi dai hakan ne ya jefa Amrah a lalurin sickler, wanda ya wahalar da rayuwarta. Tun daga sanda aka gane Amrah na da sickler, bata ta'ba jera wata biyu cikakku da lafiya ba. Wannan rayuwar abun tsoro ce, mutuwa bata alerting take zuwa, babu zato babu tsammani take riskar bawa, ta d'auke sa. Amma da dama mutanen yanzu sun kasa zama na 'kwarai. Sun kasa jin tsoron had'uwarsu da mahaliccinsu. Munanan ayyuka 'kara yawaita kawai suke. Rashin imani da rashin tausayi k'ara ta'azzara kawai suke. Wallahi duk wanda zai ji rayuwar Amrah, in dai zuciyarsa mai imani ce dole zai girgiza, dole zai k'ara jin tsoron Allah. Duk yanda 'karshenta ya yi kyau, amma hakan bai hana al'ummah da dama kokawa da mutuwarta ba. To ina ga wanda suka kasance suna aikata mummuna? Wanda babu kyautatawa a zamantakewarsu? Ya Allah! Ka ji k'an Amrah, Ka ji k'an duk wanda suka rigaye mu gidan gaskiya. Idan tamu ta zo, Ka sa mu cika da imani." Ko da ya gama wannan maganar, baki d'aya jikinsu ya 'kara yin sanyi. Ummah jin abun take kamar yanzu Amrah ta rasu. Bata san ranar da wannan rasuwar zata goge daga zuciyarta ba. Bata san sanda zata daina kukan rashin Amrah ba. "Rashin Amrah ba wai naku ba ne ku kad'ai, Abba. Rashi ne wanda ya shafi dukkan al'ummah. Domin kuwa inda Amrah tana raye, na tabbata mutanen da zasu amfana da iliminta yawa ne da su. Mutanen da zasu k'aru da ita suna da yawa. Sai dai kuma kash! Allah'n da Ya yi ta, Shi ya ga dacewar karb'ar abarSa a daidai lokacin. " "Haka ne Maryama. Ina ji a jikina ke alheri ce. Allah Ya miki albarka, Ya albarkaci karatunki da kuma rayuwarki gaba d'aya." "Ameen, Umma." Ta furta bayan ta share k'walla. "Bara na tafi. Na hana ki aiki ko girki baki yi ba. Ga shi rana ta yi tuni." "Babu komai ai. Sai na ji ki." Umma ta fad'a had'e da raka ta har bakin k'ofa sannan ta dawo. Alk'awarin da Maryama ta mata ta fad'a wa Mallam. Shi kanshi ya ji dad'i sosai, ya kuma yarda da yarinyar d'ari bisa d'ari. _A ko wane lokaci Allah Yana jarrabtar bawanSa, dan Ya ga shin zai haye wannan jarabawar ko kuwa ba zai haye ba? Rayuwar nan bata da tabbas. Sai muna dagewa da aikata kyakkyawa, ko zamu samu dacewa ranar gobe k'iyama. Allah Ya bamu ikon cinye jarabawoyinmu, Allah Ya sa mu yi kyakkyawan k'arshe._ *Tighten your belts, readers. This is just the beggining.* *Annur Iqra Al-Hussain ya zaka yi haka? Ya mutuwa zata mantar da kai mutanen da suke da matuk'ar daraja a rayuwarka? Me ya sa zaka fad'a irin rayuwar da ba taka ba, wacce bata cancanta da rayuwarka ba ko kadan?* *Shin Ina Sans yake?* *Wannan amsoshin duka zaku same su in dai kuka ci gaba da kasancewa tare da wannan littafin.* Pinky durling💗 *RAZ 2* [8/30, 3:43 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 2⃣3⃣ Gaisuwa ta musamman ga Ibrahim Lawal Zaria. Ina matu'kar jin da'din yanda kake bibiyar wannan labarin, kake bada lokacinka wurin karanta shi. Na gode kwarai da wannan kulawa. Allahu Ya bar zumunci. *** A hanzarce Maryama ta tsayar da napep kai tsaye ta kwatanta masa Islamiyyarsu. A zuciyarta tunane tunane kawai take. Tana ji a zuciyarta ba zata ta'ba barin maganar nan ba. Zata ci gaba da bibiyar rayuwar Annur, zata ga iya gudun ruwansa. Idan ma ya yi losing memory d'insa ne zata yi duk ma yanda zata iya dan ganin tunani da hankalinsa ya dawo. Har suka iso bakin Islamiyyar ma bata san sun iso ba, sau uku mai napep d'in ya mata magana sannan ta ji shi. Zumbur ta yi ta zaro kud'insa daga cikin jaka ta mik'a masa, sannan ta fito. A daidai isarta bakin gate ta d'aga kanta ta kalli sunan makarantar, gabanta ne ya mummunan fad'uwa, hankalinta ya tashi. Tunani da natsuwarta duka suka fara gushewa. Sake tuno labarin Amrah take, irin gwagwarmayar da ta sha a rayuwarta kawai take tunani. Da tafin hannunta ta share 'yar k'wallarta sannan ta 'karisa cikin makarantar. Kamar yanda ta yi tsammmani kuma haka ne, rehearzal ne ake a tsakiyar filin makarantar da aka yi rumfa ga d'alibai zazzaune, wasu kuma daga gefen da malamai suke, alamun su ne za a ma walimar. A hankali take takunta, ita d'in dama can mai natsuwa ce. Komai nata babu kuzari take yinsa. Bayan ta isa filin ne ta k'arisa wurin 'yan ajinsu, tun daga nesa Jiddah ke mata murmushi, tana gwada mata wuri a kusa da ita, alamun ta je ta zauna a can d'in. Sai da ta gaishe da malamanta sannan ta isa ta zauna, tana ma Jiddah murmushi. "Maryama sarkin hawaye. Ke babu dalili ma ionki fitar da ruwa yake. Kar dai idanuwan nan da aka zuba miki ne kike ma hawaye." Murmushi Maryama ta k'ir'kiro ta ce, "Jiddah baki da dama. Ni ban ma fa san ina wani hawaye ba, amma ke har kin gani." Jiddah ta ce, "Maryama ke nan. Miye naki zai gagare ni ganewa yanzu? Ai da ganin fuskarki an san akwai damuwa a tattare da ke. Idanuwanki kad'ai sun isa su nunar da hakan." Ajiyar zuciya Maryama ta sauke, "Haka ne, Jiddah. Tabbas ina da damuwa. Ki bari har a tashi, insha Allahu zan sanar da ke komai. Kuma ke d'in ma ina da bu'katar tallafinki." Gya'da kai Jiddah ta yi, ta ce, "Allah Ya jishe mu alkhairi to. Insha Allahu zan taimaka miki bakin k'arfina." Daga haka suka mayar da hankalinsu ga karatun da d'aya daga cikinsu take yi. Yanayin sab'ulewar jikin Maryama ya sa Mallam Yusuf ya ce mata kawai ta tafi gida, saboda shi a tunaninshi ma ko bata da lafiya ne. Bata musa masa ba, dan dama tana da buk'atar komawa gida ta natsu, ko zuciyarta zata samu salama. Alk'awari ta ma Jiddah cewa da dare zata kira ta a waya, zata sanar da ita komai. A haka suka rabu, Maryana ta kama hanyar gidansu, tun da dama babu nisa daga gidansu zuwa Islamiyyar. K'o'karin kawar da damuwarta ta yi a daidai isarta gidan. Ta fiddo wayarta daga jika ta duba 'karfe uku ne da rabi, sannan ta mayar a cikin jikar. Da sallamarta ta isa. Tun a parking space ta ci karo da motar cousin d'inta, mai suna Ahmad. Murmushi ta saki lokacin da ta ji muryarsa ta amsa sallamar, ta k'arisa ciki da fad'in, "Wata mota nake gani kamar ta Ya Deedah." Bai ce mata komai ba sai harararta da ya yi cikin wasa, yana binta da kallo. "To kallon kuma na menene?" Ta furta bayan ta ajiye jikarta bisa kujera. "Sannu da gida, Mama." "Maryama, an dawo? Amma kun tashi da wuri." Mamar tata ta fad'a tana duba agogon bango. "Mama bana d'an jin dad'in jikina ne, Mallam ya sallame ni." "Subhanallahi! Me ya same ki?" Mama ta fad'a cike da damuwa a fuskarta. "Ciwon kai ne Mama. Ga kuma zazzab'i zazzab'i da nake ji yana sauko min." Deedah ya ce, "To ko lokacin tafiyar ya yi ne? Sai mu fara tanadin geron gumba." Hijabin da ta cire ta jefa masa, ta turo bakinta tana fad'in, "Sai ka riga ni ai." "Yanzu dai je ki zuba abinci ki ci, sai ki sha magani." To kawai ta fad'a ba tare da ta tashi ba. Ganin bata da niyyar tashi ya sa Mama ta mik'e da kanta tana furta, "Bara na zubo miki da kaina, kuma zan tasa ki gaba har sai kin cinye shi tas. Dan na san halinki ke d'in nan abinci ba damunki ya yi ba." Bata jira ta furta komai ba kawai ta fice, had'e da nufan kitchen. Kamar jira Maryama ke yi ta tashi, ta ce, "Dan Allah Yaya dama akwai tambayar da nake so na maka. Seriously a cire maganan wasa." "To ina jin ki." Ya fad'a tare da mayar da baki d'aya hankalinsa gare ta. "Wai ka san wani wanda ake ce ma Annur Iqrah Al-Hussain?" Cike da mamakinsa ya zaro ido yana kallonta, bai iya furta komai ba sai dai da zarar an kalle sa za a san yana cikin mamaki. "Tambayarka nake fa Yaya. Ka bani amsa mana." Ta fa'da tana kallonshi. Da k'yar ya iya furta, "To ke Maryama me ya ha'da ki da wannan d'an iskan yaron?" "'Dan iska?" Ta jinjina har yanzu bata daina kallonsa ba. "Ehh k'warai kuwa d'an iska. Wannan yaron wanda ya yi k'aurin suna wurin lalata yaran mutane? Annur na amfani da damar dukiya da suke da ita, yake yaudarar y'an mata. Wallahi Maryama zan iya ce miki, tun da nake a rayuwata ban tab'a ganin mashayin yaro kamarsa ba. Ba zan tab'a manta wata rana ba... *** _Wasu matasa ne tafe cikin halin maye, ko wannensu ya sha ya yi tatul, tafiya suke amma kamar zasu fa'di, sai layi suke._ _Suna isowa bakin wani shago suka ci burki, ciki suka shiga har suna 'kok'arin buge kwalayen da ke jere a wurin._ _Mai tsaron shagon ya taso a tsorace yana fad'in,_ _"Me ya shigo da ku shagona? Ku fice min tun ban kira maku y'an sanda ba. Wato irinku ne masu zuwa suna kalle yanda shago yake, dan su biyo dare su yi sata ko? To wallahi asirinku ya tonu. Baku isa ba"._ _Dariya kawai suka fashe da ita. Suka kalli junansu cikin halin ko in kula. K'ok'arin ruftowa cikin shagon kawai suke._ _Sake dakatar da su ya yi a karo na biyu, yana k'ok'arin ture su da hannuwansa, 'kok'arin fad'uwa suka yi, saboda duk wanda yake cikin maye ba wani k'arfin kirki yake da shi ba._ _Suna cikin haka sai ga Annur ya shigo, a yanayinsa kawai aka kalla za a tabbatar da shi d'in kanshi a buge yake, sai dai nashi mayen ya sha banban da na wancan, saboda shi slow ne kawai yake, hankalinsa bai fita ba._ _Tambayar mai shagon ya yi abin da yake faruwa, nan mai shago ya kwashe komai ya sanar masa, a k'arshe ya ce yana daf da tara masu mutane in har basu fice masa daga shago ba._ _Annurr na jin haka ya dakatar da mai shagon, cike da gadara yake fad'in,_ _"Duka shagon naka tsiyar nawa ce a cikinsa? Ka yo masa ku'di ka ga idan ban siye kaf ilahirinsa ba. Amma ka tasa bayin Allah gaba kana k'ok'arin yin dambe da su, ka ci zarafinsu. To ni d'in nan da kake gani na k'i jinin in ga ana cin zarafin masu shaye shaye, dan duk yanda ban sansu ba sai na yi bakin k'ok'arina na ganin na mayar da martani."_ _kallon junansu suka yi, cikin muryar maye d'ayan ya ce,_ _"Abokina...wannan...wannan ma da alama na hannu ne..." dariya ta ci 'karfinsa har yana dafe cikinsa._ _Ganin haka ya sa Annur ya murmusa, ya kama su a natse ya kai su har bakin motarsa._ *** Kad'an daga halayen Annur Iqrah Al-Hussain ke nan na fad'a miki, Maryama. Yana d'aya daga cikin matasan da suke yad'a fasadi a cikin garin nan. Annur na d'aya daga cikin masu gurb'atar da rayuwar matasan Katsina. Annur da kike ji da gani, ba wai a shaye shaye kad'ai abun nasa ya tsaya ba, har da neman mata. *** _wasu y'an mata ne su biyu ke tafiya, su dukansu rik'ak'kun masu zaman kansu ne (Farha da Zee, na cikin *WANDA YA DAKA RAWAR WANI).* Fira sosai suke yi, ko wace na ba k'awarta labarin sabon dadironta. A cikin labarin nasu ne har suka kai ga'bar da Annur ya shigo cikin labarin. D'ayar ke fad'in yanda ya zo har gidanta ya da'uke ta, ya kai ta wani gidanshi da ke unguwar Madawaki. Take fad'in yanda ya kula da ita, ya kuma kashe mata kud'i masu tsoka. A k'arshe ma har da kyautar mota ya bata, saboda Annur matashi ne da ku'di._ _Jin haka ya sa k'awar ta hau kishi, saboda ita d'in ma haka ya kashe mata. Amma a ganinta, ta ya wanda take so zai so k'awarta Farha? Ai ta fi k'arfin nan. Ta fi k'arfi da ajin Farha._ _Hakan ya sa kamar wasa suka hau fad'a a tsakiyar hanya. Abu wasa ba wasa ba fad'a ya yi nisa. To fad'an karuwai dai kowa ya sanshi, hakan ya sa aka rasa mai raba su, aka barsu su kashe kansu._ _Dambe sosai suke yi, cikin dabara Zee ta samu ta zuge jakarta ta fiddo y'ar k'aramar wu'kar da bata rabuwa da ita saboda tsaro. Farha bata ankara ba kawai ta ji wuk'a a kunnenta._ _Bala'i ta ji ita kuma ta ja tsoron gashi guda na Zee, bata sake shi ba sai da ta ciro shi baki d'aya, kan ya d'auki jini. Ita kuwa kad'an ya rage kunnenta guda ya cire, sai lilo yake jini na zirara._ _A daidai lokacin sai ga Annur ya iso. Ganin halin da suke ciki ko kad'an bai sa ya tausaya masu ba. Sai ma rufe su da masifa da ya yi, yana fad'in babu shi babu su, dan haka ko sunansa ya sake ji a bakin d'aya daga cikinsu, sai ya ba'tar da ita._ *** Kinga kuwa, Annur babu ta inda aka barsa. Lalata mata, shaye shaye da duk wani aiki na b'arna yake goyar wa baya. Ko nawa ne zai iya kashewa don ci gaban lalata. Shi ya sa na yi mamakin jin sunansa a bakinki ai. Nake fatan Allah ya sa ba wani abu ne a tsakaninku ba." Deedah na kaiwa nan ya dakata, yana kallon yanda baki d'aya reaction d'in Maryama yake. Suna cikin haka ne Mama ta iso, da plate rik'e a hannunta ta furta, "Kin ji ni shiru, sai da na d'und'uma miki miyar yanda zaki fi jin dad'inta. Na kuma biya ta d'aki na d'auko miki magani. Ungo gashi." Ta mik'a mata. Karb'a ta yi, tana k'ok'arin kaiwa a baki amma tana tuna kalaman Deedah. Tana cikin haka ne Deedah ya mik'e, "Ni zan wuce, Mama. Maryama, Allah ya sawak'e." K'ok'arin kai spoon ta yi bakinta, da abinci a ciki ta furta, "Ameen, Yaya Deedah. Zan kira ka mu k'arisa maganar a waya." "To babu damuwa. Mama, a gaishe da Baba idan ya dawo." Ya tafi. Tuttura abincin kawai take ba wai dan tana jin dad'insa ba. Kawai dan ta san dole sai Mama ta takura mata sai ta ci. Bayan ta gama ta b'alli panadol ta sha, sannan ta mik'e ta nufi d'akinta. Zuciyarta cike take da tunanin yanda zata yi. Tana tunanin mafita, dan a zahirin gaskiya bata jin zata iya barin wannan maganar. Bata jin zata iya barin Annur a halin da yake ciki, wanda take ga kaman soyayya ce ta jefa shi a ciki. Tunani take yi lallai akwai gwagwarmaya babba a gabanta. To ta yaya ma zata fara? _my exam is around the corner, second to the last semester in the University. Please include me in your prayers. Thanks._ Pinky durling💗 *RAZ 2* [8/30, 3:43 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 2⃣4⃣ Da dare bayan Maryama ta samu natsuwa ba laifi, Muhammad ya shigo ta koya masa karatu. Bayan ya fita ta d'auki wayarta ta latsa kiran Jiddah. Bata b'ata lokaci ba kuwa ta d'auki wayar suka gaisa ta mata ya jiki? Nan Maryama ta kwashe komai ta sanar da ita. Daga 'karshe ta ce, "Jiddah ina son na taimaki Annur. Ina so na fitar da shi daga halaka. Duk ma yanda zan yi, ina son ganin ya fita daga mummunan k'angin da soyayya ta jefa shi a ciki. Sai dai kuma ban san ya zan yi ba. Ban san ta ina zan fara wannnn gagarumin aikin ba." Ta k'arisa maganar da dafe kanta kamar tana gaban Maryaman ne. Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke kafin ta ce, "Na san Annur, na san waye shi. Na san wasu daga cikin munanan halayensa, domin kuwa ni d'in ma ya tab'a gwada min... *** "Assalamu alaikum." Ta furta a daidai shigarta cikin gidan. Shiru ba a amsa mata ba, hakan ya bata damar sake yin wata sallamar a karo na biyu. A nan d'in ma shiru ne, sai ta samu kanta da shigewa ciki kawai, ba tare da ta jira an amsa sallamar tata ba. Zaune ta same shi a tsakiyar falo, ya tasa shisha gaba sai zuk'a yake, yana fitar da hayak'i daga cikin bakinsa. Duk'ar da kanta ta yi k'asa, a zuciyarta tana mai tir ha'de da allawadai da munanan halaye irin na Annur. Inda ta san shi zata tarar, da bata zo ba, dan da alama Hajiya Suhailar ma bata gidan. Mik'ewa ta yi a fusace zata fita, ta jiyo muryarsa ya ce, "K'anwata, Jiddah." Samun kanta ta yi da dakatawa, ba tare da ta waiwayowa ba ta ce, "Momy na ciki ne?" "Bata nan, sun je dubiya, k'anwar mai aikinta ce bata da lafiya suka tafi tare. Ni kad'ai ne a gidan." Jin haka ya sa ta ce, "To bara na tafi. Dama Mami ce ta aiko ni, idan ta dawo ka ce mata na zo, gobe zan dawo idan Allah Ya kai mu." Tana gama fad'in haka ta fara takunta, taku mai cike da natsuwa, wanda idan tana yinsa dukkan gab'ob'in jikinta sai sun motsa, ba wai kuma da gangan take yinsa ba. Halittar Jiddah ke nan. Bata ankara ba ta jiyo takunsa, yana ajje tafukan k'afafuwansa a duk inda ta d'auke nata, har ma yana neman wuce ta. Kamo mayafin da ta yane kanta ya yi, a hankali ta dakata, gabanta sai dukan uku-uku yake, ta gagara furta komai. "Me ya sa zaki tafi? Lets enjoy together mana, kafin Momy ta dawo. Akwai flavor mai dad'i a ciki." Ya k'arisa maganar da kwantaccen murmushi bisa kyakkyawar fuskarsa, wadda asalinta jajur take, amma mugun shaye shayensa ya sa ya zama bak'in k'arfi da yaji, lab'bansa su suka fi komai zama bak'ak'e. A fusace ta d'ora idanuwanta saman nashi, ta fara jefa masa kallon uku saura kwata, a zuciyarta kuwa, tunanin yanda zata yi da shi kawai take. A zuciyarta, ta k'i jinin mugayen halayen Annur. Ta k'i jinin namiji ya tab'a ko mayafinta, ballantana ya yi yun'kurin tab'a fatar jikinta. "Ka sake ni, Ya Noor..." ta fad'a tana k'ok'arin ci gaba, "Ka sake ni na fad'a maka. An fad'a maka ni ma irin y'an iskan matan nan ne, wanda kake hul'da da su?" Ta ci burki a nan, bakinta yana son ci gaba da magana, amma ya gagara furta komai, kaf ilahirin gangar jikinta karkarwa kawai take. "Haba mana Jiddah! Kar ki gwada min rashin wayewarki mana. Ni a tunanina kin waye, amma zaki watsa min k'asa a ido." "Wallahi idan baka sake ni ba, zan maka duk abin da nake ga kaman shi ya dace da kai. Ka sanni, ka san wacece ni, ka san bana tolerating nonsesnses." Sakinta ya yi, yana mai duk'ar da kansa 'kasa, yatsunsa na dama dunk'ule suke, lab'bansa suna rawa, da alama kalamanta sam! Basu masa dad'i ba. "Lemmi tell you for the last time..." ta murza yatsarta babba da ta tsakiya, ta ci gaba da fad'in, "Kar ka sake gigin tab'a ni, ko da wasa. Bana jin akwai wani abu da ya rage tsakanina da kai, ka sani. Ka fita daga harkata, ka fita daga rayuwata. An fad'a maka ni ko soyayya zan yi, zan yi ta da mutum irinka ne? An fad'a maka, kana sahun mutanen da nake jin zan iya yin soyayya da su ne? Abeg, Ya Noor, ka rabu da ni, akwai banbancin halaye da dama a tsakaninmu." Cikin halin ko in kula ya ta'be bakinsa,ya d'aga kafa'dunsa duka biyun, wanda ke nunar da ko a jikinsa, ya koma mazauninsa ya zauna, yana mai ci gaba da zuk'ar shisha, cikin wani salo, mai nunar da k'warewarsa ta wannan fannin. Ita kuwa Jiddah ta fita, a zuciyarta tir kawai take da halayen Annur, yanda ya yi k'aurin suna a cikin garin, kowa ya bu'de baki baya fad'in abin alkhairi a kansa. Amma a ganinta, iyayensa ne manyan masu laifi, a ce wai kawai dan baka son ganin damuwar d'anka, sai ka kasa kwa'barsa yayin da ya tafka babban shirme? A k'alla, Annur zai yi shekara ashirin da takwas yanzu, ina yake da yarintar da za a ce wai ba za a kwab'e sa ba? Kullum bad'alarsa k'ara yawa kawai take. Gashi abun har ya dawo kanta. Ta sani, ya jima yana sonta, tun kusan shekara d'aya da ta gabata, yake nunar da yana sonta, amma take basarwa, take nuna bata sonshi, ba dan komai ba, sai dan gudun 'bacin suna, saboda duk yarinyar da aka ga tana soyayya da Annur, an san ba ta kirki ba ce, idan ma ta kirkin ce, to zata lalace. *** Mamanshi k'awar Mami ce sosai, tun suna yara suke tare. Hatta soyayyarsa da Amrah na sani. Na san yanda ya sadaukar da rayuwarsa a kanta, ita ma kuma haka. Na san sanda yake da halayen kirki, yake kyautata wa kowa. Na san lokacin da ya haukace, saboda har gano shi mun yi. Amma daga tashinsa cutar hauka, halayensa suka koma haka." Jinjina kai Maryama ta yi, cike da damuwa ta ce, "To yanzu Jiddah, ta ina zan fara? Please ki bani shawara, wace hanya kike ga kamar zan bi, in ceto rayuwar Annur?" Shiru Jiddah ta yi na wani lokaci, kafin ta ce, "Da zaki bi ta tawa, Maryama da kin fita sabgar da bata shafi rayuwarki ba. Da kin fita daga rayuwar mutumin da bata cancanci ki shige ta ba. In dan Amrah kike ga zaki taimaka masa, ko kin manta ita d'in ta rasu, tata ta k'are? Kin manta cewa ta yi kyakkyawan k'arshe ita kam? Shi kuma fa, babu ruwan Allah fa. Allah kama Shi zai yi matuk'ar ya mutu da wannan bak'ak'en halayen..." Bata rufe baki ba Maryama ta ce, "Saboda hakan nake so na ceto sa, Jiddah. Ina son Annur ya samu rabauta, ina so ya yi kyakkyawan k'arshe, kamar yanda masoyiyarsa ta yi." Dafe kai Jiddah ta yi, ta san halin Maryama sarai, ta san cewa ba zata tab'a fahimtarta ba, in dai tana son abu, to fa babu wasa. "Ina ga kamar ki fitar da rana sai mu je gidansu." "Zuwan gidan nasu zai sama min mafita, Jiddah?" Maryama ta d'aga lab'banta, ta ajje wannan kalaman, cike da tabbatar da kalaman, a cikin zuciyarta. "Ehh to, mu dai je. Idan muka je, zan shaida ma Momy ke 'kawata ce. Kin ga daga nan sai mu ringa zuwa akai-akai muna gaishe ta, har mu samu mafita." "Good idea, Jiddah. Hakan za a yi. Amma gobe idan mun ha'du a Islamiyya, sai mu 'kara tattaunawa." "To babu damuwa. Allah Ya kai mu." Daga nan suka tsinke wayar, Maryama na jin zuciyarta na d'an samun sassuuci. A hankali ta runtse idanuwanta, ba wai bacci take ji ba. Tana tunanin gwagwarmayar da ke gabanta ne. Tana ji cewa ba fa k'aramin risky ba ne zata jefa rayuwarta a ciki. Shiga rayuwar mutum irin Annur, ba abu ne mai sau'ki ba. A haka b'arawo bacci ya sace ta, bacci mai nauyi ya d'auke ta, wanda ke cike da mafarkai kala kala, duka kuma sun shafi abin da ta saka a gabanta. Washe gari ta shirya aka kai su makaranta, a mota Muhammad ke mata firar, "Yaya Maryama, jiya fa Mallam Isma'eel ya sake bani sak'o wurinki, wai in gaishe ki, kuma wai ki bada lambar wayarki a kai masa..." Bai rufe baki ba Maryama ta d'aure fuska tana kallonsa, tsaki ta fara yi kafin ta ce "Wai kai ba na ce ka ce masa ya fita harkana ba? Yo wai ina dalili. Malamin Islamiyya amma sai mugun son 'yan matan tsiya. Daga zuwa sau d'aya ya nace ma aiko ka wurina. To ka fa'da masa ni ina da mijina." D"aure fuska Muhammad ya yi, shi a dole ya ji haushi ta ce bata son malaminsu, murya k'asa k'asa ya ce, "Yaya Maryama ina mijin naki yake? Ni ai ban san akwai shi ba." Hannayensa ta ha'de duka biyu, babu annuri ta ce, "Wai me ke damunka ne? Bana son yawan surutu, kuma ka sani. Ka fa'da masa abin da na fad'a maka." Bai ce ,komai ba sai zumb'urar bakinsa da ya yi har suka isa bakin makarantarsu, sauke ta aka yi, ta ma dreban nasu bankwana ta tafi, ba tare da sun yi bankwana da Muhammad ba kaman yanda suka saba. Bayan ta shiga cikin aji ne ta samu Jiddah ce kawai zaune tana maimaita inda zata karanta a saukarsu. Da fara'a ta shiga, ya mik'a mata hannu suka gaisa sannan ta zauna a kusa da ita. "Bakinki yana motsi, kamar kina son yin magana." Jidda ta furta tana kallon Maryama da ke k'ok'arin zaro wayarta daga cikin jika, tana jin tana ringing. "Ina zuwa." Ta fa'da had'e da latsa wayar, ta lumshe idonta, ta bu'de a hankali tana sauraren kalamansa da suke dira a saman kunnuwanta. "Bobby, na fad'a maka ka fita harkata, na san ka san bana son kirana da kake ko? Please ka daina mana. Ko ana soyayya dole ne?" Tauna lab'bansa ya yi, cikin wata murya ya ce, "Ba a soyayya dole, amma dole ki kula ni, Maryam. Ba zan iya rayuwa ba tare da ke ba, na san kin sani, bakya buk'atar maimaici. A ganina kamar kina b'ata wa kanki lokaci ne, kina asarar yawun bakinki." "Dakata! Bobby. Na san ka san cewa ruwa ba sa'an kwando ba ne. Me zai sa na so ka bayan halayenka basu kasance na gari ba? A kan me zan so mutumin da bai san darajar mutane ba? Na rok'e ka, Bobby. Dan Allah ka k'yale ni haka nan. Ka bar Maryama ta samu sa'ida mana." Ta tsinke wayar, zuciyarta sai tafarfasa take, tana mai tsananin jin haushin Bobby. "Calm down..." Jidda ta fad'a tana dafa kafad'ar Maryama. "Na san Bobby, ko ba Farouk Sardauna ba?" Cike da mamaki ta kalli Jiddah, da idanuwa ta bata amsa. "Abokin Annur ne, ina nufin Ya Noor. Na sha ganinsu tare, wani lokacin idan na je gidansu. Amma ke me ya had'a ki da shi?" Lab'banta duka biyun ta tura a cikin baki, ta d'an tsotse su kafin ta furzar da iska daga bakinta, ta ce, "A makaranta muka had'u... *** Trecking suke ita da 'kawarta Hannatu, tafiya suke suna hirar gajiyar da suka yi, kasantuwar tun daga department d'insu suke tafiya da k'afarsu, har gasu sun iso bakin gate amma basu samu abin hawa ba. Lakcar 'karfe shida ce suka yi, kuma dama sukan samu irin wannan matsalar a duk lokacin da suka yi ta. Maryama ce ta ce, "Na matuk'ar gajiya wallahi. Gashi abun hawa ya yi wahala. Idan ma yanzu muka ci sa'a school bus ta zo, hanga ki ga tarin d'alibai, wanda duk abun hawa suke jira fa. Ta ya zamu samu wuri?" Hannatu ta bud'e baki zata yi magana ke nan suka hangi bus na k'aratowa. A hanzarce ta kama hannun Maryama tana fad'in, "Ki saki jikinki mu yi tafiya, Maryama. Dan zamu iya rasa wuri." Saurin da suke yi ne ya sa Maryama ta yi tuntu'be da robar lemo, wadda aka yar a hanya. K'wace hannunta ta yi daga na Hannatu, fuskarta na nunar da damuwa, tana k'ok'arin yin magana. Kallon da ya ajje a setin fuskarta ne ya dakatar da ita daga maganar da ta yi niyyar yi. Bai d'auke idonshi daga nata ba, haka ita ma bata d'auke nata daga gare shi ba. "Haba mana Maryama. Dan Allah ki zo mu tafi haba! Ki duba ki ga ko a haka har motar ta cika. Ki saki jiki mu yi tafiya wata k'ila mu samu wuri ko a tsaye ne." "Ba zan iya ba, ba zan iya sauri ba Hannah. Kin sani, babu wuya zan iya fad'uwa, a irin saurin nan da kika saka ni." "Ni ban san irinki ba, Maryam. Yanzu idan bamu samu wuri ba, ya kike so mu yi? Da k'afa kike son mu isa gida?" "Ni zan kai ku, please ki bi mun ita a hankali. Matata bata son tsanani, kin sani. Komai nata a natse ne, natsatssiya ce." Kallon mamaki Maryama ta bi shi da shi, tana son sanin yanda aka yi ta zama matarshi, tana son ta san shin a ina ma ya santa? Ita dai ta san bata ko tab'a ko ganin fuskarsa ba, sai yanzu. "Yes. Ni zan kai ku har gida." Ya furta cikin halin ko in kula, kamar da gaske dama ya santa. "Yamma na yi, ku zo mu tafi mana." Har ga Allah Hannatu ta zata da gaske Maryama ta sanshi, hakan ya sa ta kama hannunta, a hankali suke taku har suka isa bakin motarsa, wadda ya faka a can nesa da gate d'in makaranta, saboda tinted glass da gare ta. Kamar mutum mutumi haka Maryama ta koma, ta gagara furta komai, mamakinsa kawai take, mamakin samarin yanzu. Tana tunanin a inda ya santa, da kuma dalilinsa na kiranta da matarshi. Tun da suka kama hanya babu wanda ya furta komai, sai sautin da ke tashi a hankali yana bin wak'ar. Wayarta ce ta d'auki ruri, ko da ta duba ta ga Mamanta ce ke kira, hakan ya sa ta gaggauta d'auka tare da kallon mai motar. Kallo d'aya ya mata ya gano manufarta, ya gaggauta rage k'arar sautin, ya ringa fita a hankali. "Mun rasa abun hawa ne, Mama. Amma muna hanya yanzu haka." Ta tsinke wayar daga nan, ta d'ora kusa da hambrek na motar. D'aukar wayar ya yi, bai yi wata wata ba ya saka lambarshi a ciki, ya yi dailin take tashi ta fara ringing. Saving ya mata da Farouk Bobby, sannan ya ajje yana wani shu'umin murmushi. *** Kin ji yanda muka ha'du da shi. Ban san wani abu sosai game da shi ba, kawai dai na san shi d'in ba mutumin kirki ba ne. Ya dame ni sosai, Jiddah. Na rasa yanda zan yi da shi." Ta k'arisa maganar, da damuwa fal a saman kyakkyawar fuskarta. Murmushi Jiddah ta yi, ta d'an kalli gefen da wayarta take. D'aukowa ta yi a hankali ta bud'e datarta, duk Maryama na kallonta amma ta gagara furta komai. Ta jima a haka, har 'yan ajin nasu suka fara zuwa, kafin ta mik'o ma Maryama wayar, tana murmushi ta ce, "Ba wannan ba ne?" Karb'a Maryama ta yi ta kalli Bobby, su biyu ne a hoton, wani saurayi sanye da k'ananan kaya, jar t shirt da bak'ar pick up, sai Bobby daga gefenshi. "K'warai kuwa, shi ne." Ta fad'a cikin rawar lab'ba, kamar wani zai riga ta. D'an taunar leb'onta ta yi, ta ce, "Mun samu wata mafitar, akwai wani plan, kawo kunnenki ki ji." Magana suka yi k'asa k'asa, kafin Maryama ta murmusa, cike da k'warin guiwa take kallon Jiddah. Murmushi ta mata, wanda ke tabbatar da abin da ta fa'da mata, kafin ta jawo hannunta, ta saka a cikin nata. Duk chaptern da kuka ga na sako, ku rik'e ta, ku bibiye ta, domin kuwa tana da amfani a cikin wannan labarin. Kamar yanda na fa'da maku a wancan page d'in, cewa ku d'aure d'amararku, domin kuwa yanzu labarin ya fara. Shin wace idea ce Jiddah ta fad'a wa Maryama, wacce har ta saka ta murmusawa? Ko zasu yi nasara a kan wannan plan d'in da suke shirin shiryawa? Ku dai juri zuwa rafi, da sannu zamu kai ga gaci. Thanks all. Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:44 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 2⃣5⃣ Ranar litinin bayan Maryama ta dawo daga makaranta ta kira Jiddah, dama sun yi da ita cewa idan ta dawo zasu haɗu, saboda zasu je gidan su Annur. A hankali ta taka har bakin ɗakin Mama, ta same ta zaune tana waya, hakan ya bata damar zama bisa sofa, har lokacin da ta kammala wayar. Da fara'a a fusKarta ta ce, "Maryama, har kin ci abincin?" "Ehh, na ci, Mama. Dama fita nake son yi, zan je gidan su Jiddah." Miƙewa Mama ta yi bisa ƙafafuwanta, wayarta ta ajje bisa mirror, sannan ta tako inda Maryama take. "Ki kula da kanki." Kawai Mama ta furta, sannan ta ci gaba da taku har ta fita daga ɗakin. Murmushi Maryama ta saki. Tana matuƙar son mahaifiyarta, tana alfahari da ita ƙwarai da gaske. Baro ɗakin ta yi kai tsaye ta nufi nata, tana mai tsananin jin daɗi. A zuciyarta kuwa, zullumi ne fal, wanda ta kasa cire shi, duk kuwa da ƙwarin guiwar da Jiddah ke bata. Wanka ta sake yi, ta saka baƙar doguwar riga, wadda ta ji ado da duwatsu kalar gwaldin. Mayafin abayar ta yane kanta da shi. Bakin madubi ta tsaya ta dudduba kanta. Ba wata kwalliya ta yi ba sai man baki kawai da ta shafa, ta shafa madarar turaren VIP. Cikin kyakkyawan takunta ta fito, a hankali ta ƙariso wurin Mama. Bankwana ta mata, ta bata ɗari biyar cewa ta hau napep, saboda drebansu ya yi tafiya tare da babanta, zuwa garin Lagos. Godiya ta ma Mama, sannan ta miƙe bisa ƙafafuwanta, ta kama hanyar fita, tana jin yanda gabanta yake tsananta faɗuwa sosai ba kaɗan ba. A Ring road suka yi mahaɗa da Jiddah, a can ɗin kuma ta same ta, a tsaye take, tana kallon agogon hannunta a daidai lokacin, ga kuma waya a hannunta. Ganinsu da ta yi ya sa ta saki murmushi, ta iso inda suke, haɗe da hawa napep ɗin. Bayanin inda zasu je ta masa, a ƙarshe ta ce, "Gidan Alhaji Iqrah Al-Hussain." "Hajiya ai da haka kika ce tun farko, da baki wahalar kwatance ba. Waye zai ce bai san wannan gidan ba?" Basu kuma ce masa komai ba, sai fira da ta kaure a tsakaninsu. "Na ɗan jima a nan tsaye fa, Maryam. Ina shirin kiranki ke nan ma sai ga ku kun iso." Maryama ta ce, "Wallahi kuwa, mun ɗan haɗu da hold up ne a hanya." Ta gyara zamanta, tana son yin magana amma ta yi shiru, tana fuskantar gabanta. "Ki faɗi abin da kike son cewa." Ta tsinkayo muryar Jiddah, a daidai lokacin da hankalinta ya nemi isa can wata duniyar. "Zuciyata...zuciyata ta kasa bani ƙwarin guiwa, Jiddah. Ban san me ya sa ba, haka kawai sai gabana yake faɗuwa. Nake ga kamar wata matsala zata gitta a wannan plan ɗin namu." Tana kaiwa nan ta dakata, tana jin yanda gabanta yake tsananta faɗuwa, zuciyarta na riya mata abubuwa da dama, wanda ta kasa fahimtar komai daga ciki. "Maryam!" Jiddah ta furta tana kallon Maryama, ta saka ƴan yatsunta a cikin tafukan hannayen Maryama, tana mata kallo mai cike da ƙarfafa mata guiwa. "Matuƙar baki cire wasi-wasi a kan wannan aikin ba, tabbas za a iya samun matsala. Kin sani, kin san cewa nasara da sa'a suna tattare ga ma'aboci dagiya, juriya da kuma ƙwazo. Ki ɗauka a ranki cewa wannan wani aiki ne zaki yi, wanda sai mai himma da ƙwazo zai iya yinsa. Ki saka a ranki, cewa ke ɗin mai ƙwazon ce. Hakan ne kawai zai sa ki daina faɗuwar gaba." Duk yanda take son ɓoye rawar da jikinta yake yi gazawa ta yi, dole sai da Jiddah ta gane. "Shi ya sa kika ga tun farko na ƙoƙarta hana ki wannan aikin, saboda na sanki, na san halinki, na kuma san wacece ke. Aiki ne wanda marasa tsoro, masu dagiya, wanda suke da ƙwarin guiwa zasu yi. Ba wai ke ba Maryama. Amma tun da ke ɗin ma kika zaɓa hakan, kike ga kamar zaki iya, sai ki daure, ki daure ki cika wannan aikin ladar da kika yi alwashin yi. Allah Yana tare da ke, insha Allahu zaki dace" Murmushi Maryama ta yi, tana matuƙar jin daɗin yanda Jiddah ke ƙarfafa mata guiwa. Tana son yanda Jiddah ke goyon bayanta ɗari bisa ɗari, a kan wannan aikin da zata fara. "Na gode ƙwarai, Jiddah. Ina matuƙar ƙaunarki, ina alfahari da ke, na san kin sani ai." Kai Jiddah ta ɗaga mata, ita ɗin ma da murmushi a fuskarta, ta ce, "Yauwa ko ke fa? Ina so ki bani mamaki, ki yi aikin da nake ga kamar ba zaki iya yinsa ba. Na san you can make it, try your best, and make it, Maryama." "Deal." Maryama ta faɗa haɗe da dunƙule hannunta a cikin na Jiddah. A ƙofar gidan ya faka napep ɗin, kuɗinsa Maryama ta zaro ta miƙa masa sannan suka fita, suka ƙarisa cikin gidan. Tun a harabar gida suka ci karo da Annur, wanda ke ƙoƙarin fitowa daga motarsa. Kallo ɗaya Jiddah ta masa ta ɗauke kanta, ta san dole sai ya mata magana, hakan ya sa ta ƙara saurinta, har ta wuce Maryama. "Jiddah, amma kin san bana son saurin nan ko?" Ta faɗa cikin wata murya. Ko waigowa Jiddah bata yi ba ta ci gaba da tafiyarta, har ta ƙarisa ƙofar da zata sada ta da cikin gidan. Shi kuwa Annur gaggauta isowa inda Maryama take ya yi, yana son ya mata magana amma bai ga fuska ba, bai san dalili ba, kawai sai ya samu kansa da kasa furta mata komai. Yana ji a ranshi cewa fa yana son yi mata magana, sai dai wani ƙwarjini ya ga ta masa, wanda dole ya wuce ta, ba tare da ya ce mata komai ba. Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke, a ranta tana hamdala ga Allah, har ga Allah tsoronsa take, bata son ko kallonshi. Ƙofar da ta ga Jiddah ta shiga ta ɗora ƙafarta a kai, a hankali ta taka sai gata a babban falon gidan, wanda sanyi ya gama mamaye sa, yake fitar da wani ni'imtaccen ƙamshi, mai matuƙar daɗi, wanda ta kasa tantance ko daga ina yake fitowa. "Maryama." Ta jiyo muryar Jiddah, wadda ta dawo da ita daga duniyar da ta shagaltu a ciki, take jin ina ma zata dauwama a cikin wannan duniya, mai cike da ƙamshi, wadda irinta ke ƙara wa mutum walwala a duk halin da ya tsinci kansa. Takowa ta yi cikin natsuwa, a daidaice take ɗore ƙafafuwanta bisa lallausan kafet ɗin ɗakin, har ta ƙariso ɓangaren da kujeru suke. Zama ta yi bisa kujerar, kusa da Jiddah. Ta ɗora idanuwanta a bisa fuskar dattijuwar matar da ke zaune. Wacce ke cikin shigar alfarma, ta saka wani jan karen miski wanda aka ma ɗinkin doguwar riga, an ƙawata shi da wasu irin duwatsu masu matuƙar kyau. "Ina wuni?" Maryama ta buɗe muryarta ta fa, tana mai sakin guntun murmushi, wanda za a iya kiransa da na yaƙe. "Lafiya ƙalau fa. An zo lafiya?" Hajiya Suhaila ta furta, tana mai sakin murmushi a saman fuskarta. "Lafiya ƙalau, Momy." Maryama ta ce, wanda tana faɗin haka suka jiyo takun Annur, yana ƙoƙarin shigowa ɗakin. Kusa da Jiddah ya fara ƙoƙarin zama, amma wani wawan kallo da ta watsa masa dole ya tsayar da ƙafafuwansa, yana bin ta da wani irin kallo mai cike da ma'anoni kala daban daban. Tambayar Jidda Momy ta yi, ya mamarta? Ta shaida mata da tana lafiya ƙalau, ta ma ce a gaishe ta. Sun ɗan jima a haka, kafin Annur ya miƙe a bisa ƙafafuwansa, a zuciyarsa yana mai son kasancewa shi kaɗai da Jidda, saboda baya jin zuciyarsa zata iya haƙuri da soyayyar Jiddah da take ɗawainiya da shi, wadda ke hana shi saƙat, take takura shi, a duk sanda ya runtse idanuwanshi, yake kallonta, yake kallon kyakkyawar fuskarta. "Amm...Jiddah, please zan gan ki 2 minutes." Ya ɗaga laɓɓansa ya yi wannan furucin, yana jin yanda zuciyarsa ke tirsasa shi da bashi yaƙinin yin maganar, duk da shakkun Jiddah da yake yi. A zuciyarta bata son bin shi ɗin, sai dai kuma yana ɗaya daga cikin plan ɗin da suka shirya, haƙuri da juriyar duk wani abu da zai taso. Runtse idonta ta yi, tana jin yanda zuciyarta ke ingiza ta, tana mai shawarwarta a kan kar ta je, tunanin da take yi ba zai taɓa zama gaskiya ba. A wani ɓare na zuciyarta kuwa, ƙaryata wancan sashen yake, yana daɗa bata ƙwarin guiwa kan ta bi shi ɗin, ɗaya daga cikin nasarori ne. Tashi ta yi jiki babu ƙwari, tana jin yanda idanuwan Hajiya Suhaila ke yawo a duk gaɓoɓim jikinta, duk da bata kalle ta ba, jikinta na bata cewa murmushi ne shimfiɗe a bisa fuskar Hajiya Suhaila, saboda dama ta jima da kawo tayin Annur ga Maminta, sanin halin yaran yanzu ya sa suka watsar da zancen a inda suka yi shi. Ko ba komai Mamin Jiddah ta san Annur, ta san komai game da shi. ba zata taɓa yarda ta sadaukar da rayuwar ƴarta gare shi ba, mutumin da banda neman mata da shaye shaye babu abin da ya ajje. Bin bayansa ta yi a hankali, basu tsaya ba sai cikin lambun gidan, wanda yake ƙawace da shuke shuke kala kaka, masu matuƙar ƙayatarwa, wanda kallonsu kawai zai iya jefa mutum wata duniyar, mai cike da farin ciki da tarin ni'imomi. "Zauna, ga wuri nan." Ya furta yana kallonta, ya ɗan lumshe idanuwansa, yana mai sauke su bisa kyakkyawar surarta, wacce ta sha ado da jan material ɗinkin riga da sket. Zaman kuwa ta yi babu musu, tana mai ɗauke dubanta daga gare shi. tsarge take sosai saboda yanda ta ga yana binta da wani mayataccen kallo, mai cike da wata ma'anar ta daban. Bayan ta zauna shima ɗin ya zauna, yana jin wata irin natsuwa a tattare da shi, yana jin yanda soyayyarta ta gama mamaye zuciyarsa, ta sa shi rasa duk wata natsuwarsa, yake jin ina ma zata amince masa, da ya cika burin iyayenshi, ya aure ta, Shi ma ɗin ya zama magidanci. Sun jima suna masa maganar aure, ba wai momynsa kaɗai ba, har da mahaifinsa ma. saboda babu abin da ya rasa komai samu yake. Duk da cewa ya rasa aikinsa, ya ajje sa tun daga sanda ƙwalwarsa ta samu matsala. Babban kamfani babanshi ya buɗe a nan cikin katsina, kamfanin sarrafa ƙarafa ne, wanda ya samu ɗaukaka sosai. Suɗar laɓɓansa ya yi duka biyun a lokaci guda, sannan ya fiddo su daga cikin bakinsa, ya ɗora idanuwansa a saman fuskar Jiddah. A hankali ya fara ajje kalamansa, "Jiddah...Jiddah na sani, na san bana sahun irin mazan da kike so, kamar yanda kike shan faɗa min. Amma ki sani, tun da nake a rayuwata, ba a taɓa yin wata ƴa mace wacce nake ma irin son da nake miki ba. Na kasa dakatar da kaina daga sonki, na kasa tsayar da zuciyata daga ƙaunarki da ta jefa ni, wanda ban san sanda na afka a cikinsa ba. Ki dubi girman Allah..." "Dakata!" Jiddah ta faɗa haɗe da ɗaga masa hannu. Miƙewa ta yi tsaye ta fara taku a hankali, tana mai ƙarisowa a gabansa. "Ko zaka shekara da kalaman yaudararka, ba zasu taɓa yin tasiri a gare ni ba. Ka sani, na san waye kai, na san menene halayenka, na san komai game da kai. A kan me? Me ya sa kake ga kamar zaka iya yaudarata da narkakkun kalamanka, wanda ba zasu taɓa iya narkar da zuciyata ba? Bayan yaudara da ka ƙware a fanninta, har da ƙarya zaka min, kawai dan na so ka? Ko baka san na san Amrah ba? Amrah wacce ka so fiye da rayuwarka, ka kula da ita, fiye da yanda ka kula da kanka? Shi ne dan ƙarya zaka zo min da wata magana, wai baka taɓa son wata mace kamar ni ba?" Tana kai wa nan ta duƙa ƙasa a gabansa, ta haɗe duka hannayenta a wuri ɗaya, ta kalli cikin idonsa ta ce, "Dan Allah ka ƙyale ni haka nan, ka je ka nemi wata macen, wacce zata so ka mana. Wallahi baka gabana, bana jin ko darajar takalmin ƙafata ka yi. Na tsane ka, bana ƙaunarka!" Ta ƙarisa maganar da miƙewa tsaye, tana sake binsa da kallo, zuciyarta cike da fargaba da kuma tsoro. har ga Allah bata so hakan ba, bata so kalaman da ta jefa masa a ce sun fito daga bakinta ba. sai dai kuma bata da yanda zata yi, bata da wani zaɓin da ya wuce ta aikata hakan, matuƙar tana so haƙarsu ta cimma ruwa. A duk rayuwar da mutum ya tsinci kansa, kar ya zama mai girman kai, ko kuma wulaƙantar da mutane, saboda baka san yanda gobe zata kasance ba, baka san ya rayuwa zata yi da kai a gaba ba. ka so mutane, kai ma sai Allah Ya so ka. kar ka ƙi mutane, gudun kar kai ma Allah Ya ƙi ka. Na sani, na san kuna jin labarin wata kala, kamar mun faɗa wata duniyar, ba wacce muke cikinta, ta AMRAH NAKE SO ba. Kar ku damu, muna cikinta, cikinta dumu dumu, mun ɗan leƙa ziyara ne, ziyarar da ke ƙunshe da warwarar zare da abawa. Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:44 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 2⃣6⃣ Cikin wata irin murya ya fara magana, cike da rauni ya ɗaga laɓɓansa, ya ce, "Jiddah! Wallahi ina son ki, ina ƙaunarki, har ma ban san ta ya zan kwatanta miki ba. Na san inda a ce zaki leƙa cikin zuciyata, ki ga yanda ƙaunarki ta mamaye kaf tsokarta, da ba zaki taɓa ƙi na ba, ba zaki taɓa jifa na da wannan razanannun kalaman naki, masu razana tunanina ba..." Ya runtse idanuwansa, yana jin yanda zuciyarsa take masa ɗaci, take rinjayar tunaninsa. "...na sani, na san cewa ni ɗin ban zama mutumin kirki ba. Ban zama wani abun alfahari, wanda har zaku so ni ba. Amma ina so ki sani, wallahi da zuciya ɗaya nake sonki, da zuciya ɗaya nake da niyyar aurenki, nake son kai ki ɗakina, a matsayin matata. Dan Allah, ba dan ni ba..." Ya duƙa bisa guiwayinsa, kanshi a ɗage yana kallonta, yana kallon yanda ta haɗe rai. "Ki so ni, ba dan ni ba, ba dan munanan halaye na ba." Yana kai wa nan ya dakata, yana binta da kallo, idanuwansa sun yi jajur, wanda kaɗan ya rage su kawo ruwa, jarumta irin tasa kawai ta hana fitowarsu. "Ashe ma ka san kana da munanan halayen?" Ta faɗa tana binsa da wani mugun kallo, kallo mai cike da nuna tsantsar tsana da ƙiyayya. Shiru ya yi bai ce komai ba, sai taunar laɓɓansa da yake, yana mai takaicin halayensa, wanda ko kaɗan basu kasance na gari ba. "Dan haka tun wuri, ka nemi wacce kake ganin zata so ka, ba wai ni ba, da har in kwanta dama ta ba zan taɓa son mutum fasiƙi irinka ba." Runtse idanuwansa ya yi, yana mai jin ɗacin kalamanta, yana jin yanda zuciyarsa ke masa raɗaɗi, amma sai dai ba ya jin zai iya mata komai, ba ya jin baƙaƙen maganganunta zasu saka shi aikata mummunan aiki a kanta, kamar yanda yake ma duk macen da ta nemi kawo masa wargi a duniyarsa. "Ba zan miki dole ba, saboda ba a soyayya dole. Idan ma ana yi, bana jin zan taɓa iya yi miki dole, a komai na rayuwarki. Insha Allahu daga yau na rabu da ke, ba zan sake yi miki wata magana ta soyayya ba. Amma dan Allah ina neman wata alfarma a wurinki." Kai ta ɗaga masa alamun ya ci gaba da maganarsa, a zuciyarta tana mai tsananin jin daɗi, da alama tarkonta zai kama kurciya. Duka laɓɓansa ya saka a baki, ya kalli Jiddah bayan ya miƙe tsaye, ya ɗan sunkuyar da kansa ƙasa, ya ce, "Ƙawarki nake so. Ina nufin wadda kuka zo tare." Kasa ɓoye farin cikinta ta yi, daɗi ne ya mamaye kaf illahiri zuciyarta, ta fara ayyana abubuwa da dama a cikin zuciyarta. "Ki taimaka min ta so ni, dan Allah." Ya faɗa cikin wata murya mai rauni, wacce ba ko wane lokaci ba ne take bayyana, take fita daga bakinsa ba. "Ya Noor, ba wai kana da abin ƙi ba ne a jikinka, wanda zai sa a ƙi ka. Sai dai baƙaƙen halayenka ne abun ƙi,wanda babu na tsinta a ciki. A duk halayenka babu na kirki, babu wanda mace zata ɗauka ta so ka, ta aure ka, har ta yi alfahari da kai a matsayin mijinta." Ta koma bisa kujerar da ta sauka daga kai, ta seta idanuwanta a cikin nashi, cikin natsuwa ta ce, "Ya Noor, me zai hana ka koma asalin Annur ɗinka? Ka koma Annur ɗin da kaf duniya take alfahari da shi? Me zai hana ka kawar da duk wannan sabbin halayen da ka ɗauko cikin ƙananan shekaru, ka koma naka na asalli na shekara da shekaru? Wallahi matuƙar baka canza halaye ba, na tabbatar ba zaka taɓa samun matar kirki ba. Babu macen kirkin da zata so auren mazinacin miji. Babu wacce zata so auren miji ɗan ƙwaya, wanda zai iya illatata a ko wane lokaci. Na tabbatar Maryama ba zata ƙi ka ba, sai dai zata iya ƙin munanan halayenka. Maryama mace ce mai addini, mace ce kamila, mace ce wacce ko wane namiji zai so mallakarta a matsayin matarsa." Shiru ta yi daga nan tana kallon reaction ɗinsa, tana jin yanda tausayinsa ke dira a cikin zuciyarta. Sai dai kuma har cikin zuciyarta bata ƙaunar Annur, bata jin zata iya son shi, ba wai dan plan ɗinsu kawai ba. Hannunshi na dama ya cusa a cikin sumarsa, ya murza a hankali sannan ya fitar, yana mai dubanta, duban tsanaki ya ce, "Wallahi Jiddah bana jin zan iya barin halayen nan ne, da tuni na daina su. Na riga na zama addicted da su." A fusace ta miƙe tsaye tana binsa da wani mugun kallo, kallon da ke ƙara bayyana masa irin tsanarsa da ta yi. "To shi ke nan. Ba kuwa zaka taɓa samun ni ko ƙawata ba. Ka ga sai ka je can ka nemi wata mai irin halinka ka aura. Mu ma zamu nemi masu irin halayenmu." Tana kaiwa nan ta fara taku, takun da ke ƙara narkar da zuciyar Annur a duk sanda yake kallonta. Bai tsayar da ita ba, haka kuma bai bi ta ba. Sai dai ya rasa yanda zai yi, bai san ya zai yi da zuciyarsa ba. Ya rasa gane me yasa ya kasa cire Jiddah daga zuciyarsa, duk da irin wulaƙancin da take masa ba. Bai san me ya sa daga kallo ɗaya ya kamu da son Maryama ba. Bai ma san ya hakan ta kasnace ba. Kanshi ya haɗa da guiwoyinsa, yana jin yanda kansa ke masa zafi, yake barazanar fashewa. Zuciyarsa kuwa ya ma rasa a babin da zai saka ta. Babin ƙaunar Jiddah da ya jima yana so, ko kuwa son Maryama da ya fara daga kallo ɗaya? Farin ciki ne lulluɓe da zuciyarta, ta sani, ta san dole wani abu zai faru, ko ba yanzu ba. Da fara'a ta shiga falon, sallama ƙunshe a bakinta. Kallo guda Hajiya Suhaila ta mata ta ji wani irin daɗi a zuciyarta, dan da alama sun daidaita kansu ne, the way take murmushi. Ta kasa ɓoye farin cikinta. "Kina ta jirana, ko Maryam?" Jiddah ta faɗa bayan ta ɗauki wayarta daga kujerar da zata zauna, ta daidaita zamanta a hankali, murmsuhi bai gushe daga fuskarta ba. "Wallahi kuwa." Maryama ta faɗa tana kallon yanda ƙawar tata ke farin ciki. "Afuwan, wallahi wani abokinsa ne ya haɗa ni da shi, shi ya sa na daɗe." Tana faɗin haka tana kallon yanda fuskar Hajiya Suhaila ta sauya daga fara'ar da take zuwa wani yanayin da ba za a iya fassara irinsa ba. "Sannunku da hutawa Momy. Bara mu fara haramar komawa, lokaci na tafiya, kuma akwai Islamiyya." Jiddah ta faɗa bayan ta miƙe, tana fuskantar Momy, da fara'a a saman fuskarta. "Tun yanzu zaku tafi? Gaskiya ban gode da wannan zuwan ba, 'yata. Ya kamata a fidda min rana ta musamman, Maryama ta biyo ki ku min yini guda cur." Bayan Maryama ta miƙe ta ce, "Insha Allahu zamu fidda rana guda mu zo, Momy. Sai dai kawai ki ganmu kwatsam." Miƙewa ta yi Hajiya Suhaila, da murmushi ta ce, "Ina zuwa." Ta haura saman benen zuwa ɗakinta. Bata jima ba sai gata ta fito, hannunta riƙe da ledoji guda biyu. Miƙa wa Jiddah ta yi ta ce, "Kun zo a lokacin da uwar taku bata da komai na ƴan mata. Ga wannan, turaruka ne, kowa guda ɗaya. Na gode ƙwarai da zumunci, kuma ina sauraren zuwanku yini." Godiya sosai suka mata, sannan suka kama hanyar fita, zukatan ko waccensu da abin da take saƙawa. Tsaye yake jikin gate, ya ɗan jingina da ɗakin mai gadi, kansa sunkuye yana kallon ƙasa. Ganinsa da suka yi ya sa su kallon junansu, Maryama na tunanin yanda suka yi da Jiddah, da alama dai ta yi nasara, ta yanayin fuskarta kawai. "Ku jira zan sauke ku." Ya faɗa can ƙasa ƙasa, ba tare da ya kalli ko waccensu ba. "Ka bar shi kawai, a napep muka zo, kuma zamu hau mu koma a kanta." Jiddah ta faɗa, cikin halin ko in kula. Bai saurare ta ba kawai ya nufi parking space, dama akwai makulli a jikinsa, wata farar benz kawai ya shige, ya fara ma mai gadi horn, alamun ya buɗe masa. Lokacin da ya fita da motar har sun riga da sun fita su ma, hakan ya sa ya ci burki a gabansu, yana binsu da kallo su duka biyun. Ganin kamar basu san yana yi ba ya sa ya danna horn har sau biyu, amma babu wacce ko kai ta daga ta kalle shi. Har ya so ya yi zuciya ya ƙyale su kuma dai ya ji ba zai iya ba, ya sake danna masu wani horn ɗin, bayan ya sha gabansu. Ɗagowa ta yi Maryama ta kalle shi, sannan ta sunkuyar da kanta ƙasa, ta ci gaba da tafiyarta. Gyaɗa kansa ya yi, yana mai tsananin jin haushin kansa, kafin ya take motar a fusace, ya tafi ya bar su. "Just wait a little while, zaka sha mamaki, Annur Iqra Al-Hussaein." Jiddah ce ta yi wannan furucin, tana mai sakin murmushi, haɗe da jinjina kanta. "Tell me something, Jiddah. Da alama haɗuwarku ta tafi yanda muke so." Maryama ta faɗa da murmshi kwance a saman fuskarta. "Indeed, Maryam. Komai ya kusa kasancewa yanda muke so. An kusa zuwa inda zamu ji daɗi." Ta labarta mata kaf yanda suka yi da Annur, da halin da ya shiga ta dalilin kalamanta, da kuma ƙaunarta da ya faɗa ta lokaci guda. Fara'a sosai Maryama ta faɗaɗa, ta ma rasa me zata ce, ta rasa yanda zata nunar da farin cikinta. "Ban zaci abun zai zo da sauƙi haka ba, ko kaɗan. Ashe ma sauƙin hali gare shi." Jiddah ta gyaɗa kanta ta ce, "Waye ya faɗa miki yana da sauƙin hali? Soyayya ce kawai. Kin ma san wani abu wai?" Kai Maryama ta gyaɗa alamar a'a. "Ban taɓa tsammanin kallo guda zai sa Ya Noor ya so ki ba. Sai dai kuma na daina mamaki, saboda yanda ya goge da ƴan mata, yake matuƙar son mata. Ke, mace fa ko wace iri ce in dai zai ganta sai ya ce yana so. Ina ga fa ko taɓarya aka ɗaura ma zani da riga sai gayen can ya ce yana sonta." Ta ƙarisa maganar da dariya a fuskarta. "Ba zan musa miki ba kam. Lallai na yarda, kin san Annur." Maryama ma da dariya a fuskarta ta yi wannan maganar, har tana ɗaga hannunta alamun jinjina ga Jiddah. "Yau ana ma magana? Ai dalilin da ya sa na shirya hakan ke nan. Sanin halinsa da na yi, bashi da wasa in dai ta wurin mata ne. Ita ko Momy har ta fara jin daɗi, ta ɗauka ko daidaita kanmu ne muka yi." Tafa hannu suka yi su biyun, a daidai tsayuwar napep a gabansu. Bayan sun shiga suka kwatanta masa gidan su Jiddah, saboda can zasu fara zuwa ta yi shirin makaranta, sannan su tafi gidan su Maryama ita ma ta shirya. Suna cikin napep ɗin wayar Maryama ta yi ringing. Sunan mai kiran da ta gani ne ya sa ta murmusawa, ta kalli Jiddah da murmushi sannan ta ɗaga wayar. "Bobby." Ta faɗa a hankali, tana sauraren abin da zai faɗa. "Dan Allah Bobby ka ƙyale ni. Ni fa ina da wanda nake so, yake so na. Me zai hana kai ɗin ma ka nemi wacce zata so ka? Ina amfanin soyayyar maso wani wai?" Saukar da muryarsa ya yi, ya ce, "Ba zan taɓa daina son ki ba, kin sani. Wallahi in da a ce Allah zai haɗa ni da wannan saurayin naki, koma wanene da sai mun yi ko ni ko shi. A kan me zai nemi shiga hurumin da ba nasa ba? Rayuwarki don ni aka yi ta, dan haka ya zama dole ki so ni, ko ma ta halin ƙaƙa ne." Yana gama faɗin haka ya tsinke wayar, ba tare da Maryama ta sani ba. Jin shiru ne ya sa ta ɗago wayar ta duba, ganin ya kashe ya sa ta sauke nannauyar ajiyar zuciya, ta mayar da wayar a cikin jaka. "An zo wurin." Maryama ta furta, tana kallon Jiddah, cike da farin ciki. "Da alama plan ɗin namu ma ba wani mai tsawo ba ne. Ba da jimawa ba zamu kammala shi." Jiddah ta ce, "Na tabbata wurinsa zai je yanzu. Saboda babu mutum mafi kusanci da Ya Noor kamar Bobby. Shi ya fi hallaka rayuwar Ya Noor, shi ya sa na kawo mana wannan plan ɗin." Dunƙule hannyensu suka yi, cike da ƙaunar junansu. To readers, how was this chapter? Akwai masu tausayin Annur kuwa? Akwai masu tausayin ƙangin soyayyar da ya jefa kansa a ciki? Wai miye ribar wannan plan ɗin da Jiddah da Maryama suke ƙullawa? Zai yi tasiri kuwa? Zai gyara rayuwar Annur, ya koma asalin Annur ɗinsa? Zaku samu amsoshin wannan tambayoyin, idan har kuka juri bibiyar Amrah. Zata warware maku zare da abawa. Har abubuwan da da dama daga cikinku na san sun manta da su, duka zan gano maku su, sannu a hankali. Ina son ku irin sosai da sosai ɗin nan, kun san da haka kuwa? Soyayya fi sabilillah. Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:45 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 2⃣7⃣ Kamar yanda su Maryama suka yi tsammani kuwa haka abin ya kasance. Bayan Annur ya bar inda suke kai tsaye wurin Bobby ya nufa. A fusace ya faka motar, yana jin yanda zuciyarsa ke tafarfasa, take duka da sauri da sauri. Babu natsuwa ya iso cikin gidan su Bobby, isarsa ɗakin kuwa ko knocking babu haka ya afka ciki, babu annuri ko kaɗan a fuskarsa. "Guy, ya dai?" Bobby ya faɗa, yana kallon yanayin abokin nasa. Banza da shi Annur ɗin ya yi, yana mai ƙoƙarin jawo shisha a gabanshi. "Guy me ke damunka ne? Babu flavor a ciki ai." Tsaki ya saki bayyananne, haɗe da ture shishar daga gabansa, yana mai dafe kansa. Matsowa ya yi Bobby a kusa da Annur, ya dafa kafaɗarsa, yana son jin dalilin yanayin da yake ciki. "Abokina, am in love..." Bai ƙarisa maganar ba Bobby ya tulle da dariya, har yana riƙe cikinsa. Da hannu ya ringa gwada sa, yana son yin magana amma dariya ta fi ƙarfinsa, da ƙyar ya iya faɗin, "Kai ɗin? Kuma true love? It'll never be possible." Gyaɗa kanshi ya yi Annur, ya ƙi faɗin komai, saboda takaicin Bobby da yake. "Guy, wai da gaske kake ko da wasa? Wannan wace irin mace ce, wacce take neman jefa guy cikin tarkon ƙaunarta?" "Wallahi..." Bobby ya dakatar da shi. "Ko Jiddah ce?" "Ba Jiddah ba ce, abokina. Ta zo da wata ƙawarta ne gidanmu yanzu. Ban ma san yanda aka yi, daga kallo ɗaya na faɗa ƙaunarta ba. Lokaci ɗaya na ji ƙaunar da nake ma Jiddah, ta fara gangarowa zuwa ga ƙawar tata, wacce na ji ta ambata da Maryama. Abokina, please ka bani solution, ya zan yi ta so ni?" Ajiyar zuciya Bobby ya sauke, cikin natsuwa ya fara ajje kalamansa, "Guy, kai fa jarumi ne, na sani, kai ma kuma ka sani. Wace irin mace ce wacce kake ga kamar zata iya gagararka? A tunanina babu ita a duniyarta, ba a yi ta ba, ba kuma za a taɓa yinta ba. Yanzu dai bara na baka codein mai sanyi, ka sha ko zaka samu sassauci a zuciyarka. Daga nan sai mu je wurin wannan mutumin, duk ma yanda zai maka sai ya yi." Sassanyar murmushi Annur ya ajje a saman kyakkyawar fuskarsa, yana jinjina kai alamar gamsuwa da furucin Bobby. Deep freezer ya buɗe Bobby, ya fiddo robar coke mai sanyi ƙwarai, sannan ya rufe freezer'n, ya ƙariso gaban Annur. Jijjigata ya yi, sannan ya miƙa wa Annur, da murmushin jin daɗin yanayin da ya ga abokin nasa a daidai wannan lokacin. "Thank you very much, abokina. Am proud of you, ka sani." Ɗaga kwalbar ya yi ya kai bakinsa, bai sauke ba har sai da ya yi rabin robar, sannan ya ajje ƙasa, yana jin yanda duniyarsa ke masa daɗi, kamar ba shi ne yake cikin ɓacin rai a ƴan daƙiƙun da suka wuce ba. Bayan kamar daƙiƙa ɗaya, ya sake ɗora robar a bakinsa, sai da ya shanye tas sannan ya sauke, yana kallon Bobby da lumsassun idanuwansa. Minti talatin Annur ya ɗauka da shan coke ɗin, ya fara slow, yana jin daɗin yanayin nasa, wanda yake jin ba zai taɓa daina shiga irinsa ba, har sai sanda ya kwanta damarsa. "Guy, zaka iya tashi kuwa?" Bobby ya faɗa, bayan ya saka farar t shirt a jikinsa. "Zan iya, ɗan taimaka min na miƙe." Annur ya ce da Bobby, bayan ya janye daga bakin gadon da ya jingina da shi. Taimaka masa ya yi Bobby, ya miƙe a hankali, ya ajje ƙafafuwansa ƙasa. Makullin motarsa Bobby ya ɗauka, ya saka a aljihun wandonsa, sannan suka kama hanyar fita. Bobby da kansa ya ja motar, sauti ya kunna, kafin ya ja motar a tsiyace suka bar wurin. Tafiya suke sosai, suna yi suna ɗan taɓa hira, Annur na ɗan sako surkulle, saboda juyewar da ya yi, hankalinsa ya fara fita daga kansa, wai dan ma cyrup ne, a ganinsu ba ya gusar masu da hankali. Sun yi nisa da Katsina, har sai da suka isa wani ƙaramin ƙauye mai suna Jani, hanyar Mani. Lungu da saƙo suka hau bi, har sai da suka fita daga duk gidajen da ke cikin ƙauyen. Ta cikin gonaki suka ringa bi, sai dai ga hanyar mashin da ta mota nan, da alama ana yawan bin hanyar ne. Gaban wani gini suka ci burki, ginin jar ƙasa ne, wanda yake zagaye da wasu irin ƙayoyi, baki ɗayansa. Faka motar Bobby ya yi, ya kashe motar, sannan ya fito ya zagaya ya buɗe wa Annur, ya kama masa hannu suka shiga gidan. Tun daga bakin ƙofa Bobby ya fara magana, "Boka mai ran ƙarfe, boka gagarabadau, boka mai gani har hanji, boka mai hikima da fasaha, boka gamu gare ka, ga baƙin jiya sun dawo, sun dawo da wata gagarumar buƙata." Bobby na direwa nan sai ga wannan ƙayoyin sun fara daddarewa, suka buɗa masu hanya suka shiga ciki. Babu mamaki ko kaɗan a saman fuskokinsu, sai ma murmushin bobby da ya faɗaɗa, suka isa bakin ɗakin, wanda shi ɗin ma zagaye yake da ƙayoyi, sai mutum ya rantse cewa kango ne, babu mai rai a cikinsa. Wani kirarin Bobby ya ƙara yi masa, nan ma ƙayoyin suka ringa darewa suna basu hanya, har suka ƙarisa daga cikin ɗakin. Babu kowa a ciki, sai wani tsohon gadon ƙarfe, da wata yagulalliyar katifa bisansa. Suna zama sai ga wani irin baƙin tsoho ya ɓullo a gabansu, baki ɗaya fuskarsa ta ko ina suma ce fara tas, wacce za a iya kiranta da furfura. Yana daidaita zamansa kuma wata ƙwarya ta ɓullo a gabansa, cike da jini a cikinta. Bai ce masu komai ba, amma sun san abun da zasu yi. Bobby ya fara ɗaukar ƙwaryar ya sha jinin da ke ciki, sannan ya miƴa wa Annur ma ya sha, suka rage kaɗan a ciki. Shi ma bokan ɗauka ya yi ya sha, bai sauke ba sai da ya shanye jinin tas, sannan ya ajje a ƙasa. Yana ajje ta kuma ta ɓace ma ganinsu. Kallon Annur ya yi cikin ido, ya zaro masa idanuwansa masu ban tsoro, launinsu ja, ƙwayar idon kuwa da wani irin fari a cikinta, wanda ya ƙara ma fuskar tasa ban tsoro. "A duk cikin sharuɗɗan da na gindaya maku, babu soyayya ta gaskiya. Me ya sa kake son ƴan matan biyu, kuma kake son su da gaskiyarka?" Shiru Annur ya yi, yana jin jikinsa na karkarwa, laɓɓansa na rawa, ya gagara furta komai. "Na san abin da ya kawo ku. Kana so na cusa wa ƴan matan sonka ta ƙarfi da yaji, saboda kana ƙaunarsu, kuma kana son ka aure su. Haka ne!?" A daburce Annur ya ɗaga kansa, gabansa sai faɗuwa yake. "Komai zai iya lalacewa ta dalilin haka. Babu alkhairi a soyayyar da kake ma duka biyunsu. Ka sani, tun farkon aikinmu da kai, na faɗa maka kar ka kuskura ka yi soyayya ta gaskiya, ita ce tonuwar asirinka. Me ya sa ka kasa tanƙwara zuciyarka?" Cikin murya ƙasa ƙasa Bobby ya ce, "A yi haƙuri boka gagarabadau, sharrin zuciya ne, ka san bata da ƙashi. A taimaka mana." Shiru bokan ya yi daga nan, ya fara tsaface tsaface da tafukan hannayensa, yana zane da hannun damansa bisa tafin na hagun. A hankali ya juyo da hannun gare su, yana faɗin, "Kun gani? Matuƙar na yi tsafi hannuna ya yi haske, to babu sa'a a cikin tsafin nawa. Gashi kuma hannun ya yi haske. Bani da wani abu da zan iya yi maku har sai sanda ka fitar da soyayyarsu daga cikin zuciyarka. Sanda duk ka shirya, sai ku dawo, zan yi ƙoƙarin gyara ɗaurin da ka so kwancewa." Shiru suka yi su duka biyun, suna bin bokan nasu da kallo, kafin a hankali Annur ya ce, "Zan ƙoƙarta ya bokana! Ko dan gudun ɓallowar wata maganar. Ina neman taimakon boka da ya agaza min, ya bani taimakon da zan yakice soyaygarsu daga zuciyata." Zane ya sake yi a tafin hannunsa, kafin ya ɗan murmusa kaɗan alamun nasara ya juyo da tafin hannunsa saitinsu. Jajur suka ga hannun nasa, hakan ya sa su yin murmushi a tare, suka kalli junansu alamun jin daɗi. "A nan dai ka yi sa'a, aljannu sun yarda, zasu taimaka maka." Ya haɗa hannayensa guda biyu, ya ɗora su a ƙasa, ya ringa faɗin wasu kalamai, wanda jinsu kawai zai iya rikitar da mutum. A hankali ya ɗago hannuwan nasa, ya buɗe su. Wani irin jan gari ne ya fito daga hannun nasa, ya runtse idanuwansa, sannan ya ce, "Rufe idonka." Rufewar kuwa Annur ya yi, yana sauraren abin da bokan zai yi masa. Saukar garin ya ji a fuskarsa, wanda sai da ya ji wani irin ɗau! Tun daga fuskar tasa, ya ringa tafiya cikin jikinsa, ya mamaye duk gangar jikin, kafin ya isa cikin zuciyarsa. Wani irin abu ya ji ya masa nauyi a zuciyarsa, kafin a hankali ya ji yana sauka, komai nasa yana dawowa daidai. "Buɗe!" Boka ya faɗa da ƙarfi, bayan shi ɗin ma ya buɗe nashi idanuwan. Buɗewar kuwa Annur ya yi, yana jin sauyin yanayi a tattare da shi. "Ku ajje abin da zaku aje ku tafi. Bayan sati ɗaya ku dawo." Kuɗi Bobby ya zaro daga aljihunsa ya dire su a gaban boka, kafin suka miƙe a tare, suka nufi ƙofar fita. Hatta da duniyar da yake ciki sai da ya fita daga ita, ya dawo asalin tasa duniyar. Codein ɗin ya sake sa, kamar ba yanzu ya shanye kwalba ɗaya a cikin lemo ba. A wannan karon kam shi da kansa ya ja motar, yana jin daɗi matuƙa, da wahaltacciyar soyayyar da aka cire masa. "Abokina...abokina na gode ƙwarai." Ya yana kallon Bobby da fara'a a fuskarsa. "Babu godiya a tsakaninmu, na san ka sani ai." "Haka ne kam." Ya faɗa bayan ya mayar da hankalinshi ga tuƙin da yake yi. Tafiyar minti sha biyar ce ta shigo da su cikin garin Katsina. Sai da suka fara biya wa suka siya flavor na shisha kafin suka kama hanyar gidan su Bobby. "Abokina, sai na koyar da yaran can lesson, sai sun san cewa ni ba sa'ansu ba ne, ni ba irin mutanen da ake wulaƙantawa ba ne a ci riba. Wallahi! Ka ji na rantse, ba zan barsu ba." Ya saki wani mummunan murmushi, mai cike da tarin ma'anonin da shi kaɗai ya bar ma kansa saninsu. Bayan sun isa gidan su Bobby sai da suka biya cikin gidan, Annur ya gaishe da maman Bobby kafin suka nufi ɗakinsa. Ƙarƙashin gadonsa ya jawo wata ƴar jaka, wacce ke cike da kayan maye iri daban daban, masu tsada sosai kuma, irin na manyan yara. Sosai suka sha suka bugu, bayan sun gama sha kuma suka ɗora da codein. Basu jima ba bacci ya ɗauke su su duka biyun. To fa! Masu karatu. Kun ga dai yanda abin ya kasance. Me zaku iya cewa? Su Maryama zasu ci riba kuwa? Wane irin asiri ne aka masu, wanda har boka ke cewa saura ƙiris ya lalace? Wane irin mataki ne Annur ya yanke daukawar Jiddah da Maryama? Mu je zuwa dai...da sannu zaku samu amsar kaf wannan tambayoyin. Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:46 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 2⃣8 Wayarta ta jawo daga jikin caji, ta zare daga cajar, sannan ta latsa kiran Jidda, ta kanga ta a saman kunnenta na hagu. Cikin sassanyar muryarta ta ce, "Har yanzu fa bai kira ni ba, Jiddah. Ina tunanin ko dai akwai damuwa? Kar a je fa Annur ya faɗa masa komai, wata ƙila ya gano ni." Cikin kwantar da hankali Jiddah ta ce, "Ki kwantar da hankalinki, insha Allahu babu abin da zai faru. Ni ɗin ma dai Noor bai kira ni ba, to ban yi mamaki ba, saboda kin san halin mashaya, da zarar sun shiga damuwa sai su afa kayan maye, shi ne kawai suke ga zai kai su duniyar da suke so, wacce zasu samu sassauci a zuciyarsu. Ina tunanin abin da Annur ɗin ma ya yi ke nan." Shiru Maryama ta yi kamar tana son magana, bata kai ga faɗin komai ba ta sake jiyo muryar Jiddah na faɗin, "Ina ji a jikina komai zai tafi yanda muke sonsa. Zamu yi nasara da ƙarfin Allah." Sai a lokacin Maryama ta buɗe bakinta ta fara magana, cike da rauni da fargaba. "Ina fatan hakan, Jiddah. Ni yanzu abin da ma ya dame ni yanda zan tinkari Mama da maganar, tun sanda na dawo daga Islamiyya take bin kaina na faɗa mata damuwata, wai da alama akwai abin da yake damu na. Na rasa ta inda zan fara, ban saba yi ma Mamana ƙarya ba, ko na mata ma sai ta gane." Ajiyar zuciya Jiddah ta sauke, ta ɗan runtse idonta kafin ta buɗe a hankali, tana tunanin ta inda zasu ɓullo ma wannan al'amarin. "Idan har kika yi kuskuren faɗa mata komai, plan ɗinmu zai iya ɓaci, taimakon da kike son yi zai iya tsayawa, ladar da zaki samu ta kufce miki. Ba dan komai ba sai sanin da na yi babu uwar kirkin da zata ji ƴarta na neman jefa kanta a wannan risky ɗin kuma ta amince. Na san Mama, na san wacece ita, na san cewa bata son shirme, bata son duk wani abu mai wala wala. Na tabbatar ba zata taɓa barinki wannan gagarumin aikin ba." Tana dakatawa nan, Maryama ta ce, "Sanin hakan ya sa nake tambayarki mafita, Jiddah. Ban san ya zan ɓoye wannan damuwar, har Mama ta kasa ganewa ba." Jiddah ta ce, "Idan ta sake tambayarki, kar ki ɓoye mata komai game da rayuwar Amrah, ki faɗa mata duk abin da kika sani. Idan kin tashi sai ki ce tausayin Amrah ne yake azalzalar zuciyarki. Sai dai kar ki yi kuskuren kawo mata zancen lalacewar da Annur ya yi, kin san iyaye da hangen nesa, babu wuya zata iya ɗago ki." Cike da gamsuwa da wannan shawarar Maryama ta ce, "Insha Allahu hakan za a yi. Kuma na san Mama da sanyin hali, da taushin zuciya. Ita ɗin ma zata iya shiga damuwar da ta fi wacce na shiga, a lokacin da na ji labarin Amrah. Kin ga daga nan sai ta daina mamakin shiga ta damuwa." "Exactly." Jiddah ta furta cike da farin ciki. "Sannu ƙawata, Jiddah. I've nothing to say, but thank you very much. You're indeed a nice person. Allah Ya bar min ke." Ta ƙarisa maganar da lumshe idanuwa, kamar tana a gaban Jiddah ɗin ne. "It's my pleasure to make you happy, Maryam. Dan Allah bana son godiyar nan, kin sani. Kin fi ƙarfin komai a gare ni. Zan iya sadaukar da komai nawa, dan samuwar farin cikinki. Ki sani, ina tare da ke, duk tsanani, insha Allahu babu wani abu da zai faru face alkhairi. Bobby kuma..." Kafin ta faɗi abin da zata faɗi ta jiyo muryar Maryama na faɗin, "Kin ga ɗan halak! Gashi nan yana kirana." Da murna Jiddah ta ce, "Bara na kashe da sauri, kafin ta tsinke. Duk yanda kuka yi, let me know, please." "Insha Allahu." Maryama ta faɗa haɗe da tsinke wayar, tana ƙoƙarin ɗaukar ta Bobby. Kafin ta ɗauka har ta tsinke, sai dai tana tsinkewa yana sake kiranta. Ta ɗan jima bata ɗauka ba, kafin ta ɗauka cikin ruwan sanyi ta ce, "Hello." "Maryama, sarauniyar mata." Tana jin ya fadɗi haka ta ji gabanta ya faɗi, dan ta tabbatar abin da suke tunanin bai faru ba, dan inda a ce ya faru da bai kira ta da hakan ba. A wani ɓangare na zuciyarta kuma tana jin kamar lokaci ne bai yi ba, sun yi gajen haƙuri na tsammanin cikar plan ɗinsu a daidai wannan lokacin. "I can't sleep without hearing your voice, and you know." Ya ƙarisa maganar da sakin wani murmushi, mai cike da bayyanar da soyayyar da yake ma Maryama. "Dan Allah Bobby..." "Na ƙyale ki? Wai sau nawa kike son na maimaita miki? Na faɗa miki for many times cewa ba zan iya rabuwa da ke ba, ba zan iya ajje soyayyarki, ta tashi a iska ba. Me ya sa ba zaki gane hakan ba? Me ya sa kike son ina maimaici a ko wane lokaci? Dole ki so ni Maryama, dole ki koya wa kanki so na, ko ma ta halin ƙaƙa ne." Dafe kanta ta yi, tana mai jin takaicin kalamansa. Tunowa ta yi da plan ɗin nasu, hakan ya sa ta sassauta muryarta, cikin wata murya ta ce, "Bobby...Bobby ba wai bana sonka ba ne, kawai dai bana son halayenka ne. Yanzu ka ga fa, wai so na kake, amma kake min irin wannan kalaman, kake son tilasta ni, wai dole sai na so ka. Ina amfani? Ina amfanin halinka? Kai ke nan sai abokan banza, wanda suke ƙara ɓata maka suna. Yanzu kana tunanin ko na amince da soyayyarka, iyayena zasu yarda su aura maka ni, bayan sun san baka da abokan kirki?" Wani irin sanyi ya ji a zuciyarsa, ashe dai zata iya sonsa ɗin, ashe akwai ranar da irin wannan maganar ta kirki zata shiga tsakaninsa da Maryama? Murmushin gefen fuska ya yi, ya ɗan taune leɓonsa na sama kaɗan, kafin ya ce, "Babu kamarki, Maryama. I love you with all my heart. Ki dai so ni ɗin, ki amince da soyayyata, komai zai iya zuwa da sauƙi." Tafin hannunta ta sa ta ɗan shafi fuskarta, tana jin yanda kalamansa ke mata yawo a cikin zuciya. Haushinsa take ji, bata ko son jin muryarsa. Ta tsane shi, kalamansa kuwa, ƙara rura wutar tsanarsa kawai suke a cikin zuciyarta. "Na gode." Kawai ta faɗa a hankali. "Sau ɗaya tak, ki furta kina so na, I'll be glad, zan kwana ina murna, ina jin sauyi a duniyata." Janye wayar ta yi daga kunnenta, tana jin ko kaɗan ba zata iya daurewa ba, ba zata iya jurar jin kalaman nan nasa ba. Guntun tsaki ta yi a hankali, tana ƙara ɓata fuskarta, ta ce, "Ban taɓa furta wannan kalmar ga kowa ba, ba kuma zan fara a kanka ba. Ka daina tunanin ma zaka ji ta, saboda kalma ce mai matuƙar muhimmanci, wacce bata cancance ka daga gare ni ba." "Abu mai sauƙi ke nan. Na daina tunanin zan ji ta daga bakinki? To na daina. Lokacinki kawai zaki bani, na tabbatar akwai ranar da da kanki zaki furta min ita, ba wai sai na roƙe ki ba." Ajiyar zuciya ta sauke, ta ce, "Bacci nake ji, zan kwanta, please." "Zan so masoyiyata ta kwanta cikin aminci. Ki kwanta, ki yi bacci mai daɗi. Safe night." Bata ko tsaya jin wata kalamar daga gare shi ba ta tsinke wayar haɗe da dafe kanta, tana yin bayyanannen tsaki. Jiddah ta kira ta shaida mata yanda suka yi da Bobby, ta ƙara da, "Ni ina gudun samuwar matsala ne. Kar na amince masa kuma ƙalli ƙalalla ta ƙale min, Jiddah. Kin san halin irin samarin nan, babu wuya sun illata mutum. Na ma rasa me zan yi wallahi." Cikin kwantar da hankali Jiddah ta ce, "Insha Allahu babu abin da zai faru sai alkhairi. Idan ba ta wannan hanyar ba babu hanyar da nake ga zata zame mana maslaha. Saboda Farouk Sardauna ne kaɗai abokin Ya Noor wanda ya yarda da shi. Shi ne wanda suka fi sheƙe ayarsu tare. Kinga rabuwarsu ce kawai zata iya gyara rayuwar Annur, zata sa ya ji komai na banza ya fice daga duniyarsa, har ya sake waiwayarmu." Jinjina kai Maryama ta yi, a hankali ta ce, "Haka ne, Jiddah. Zan bashi lokaci tukuna, kafin na furta na amince masa. Daga nan sai a mu san miye next." "Yes, haka za a yi. Mama kuma kar ki tinkare ta da maganar can har sai idan ta sake tambayarki." "Insha Allahu. Bara na kwanta, sai da safe." Tsinke wayar suka yi su duka biyun, mafi rinjaye na zukatansu na ƙarfafa masu guiwa cewa zasu yi nasara, kaɗan ɗin zuciyarsu ne yaƙe tsayar da su. *** Wayarsa ce ta ɗauki turi, a daidai sanda ya shiga gida. Dubawa ya yi ya ga mai kiran nashi, bayyanannen tsaki ya yi haɗe da silencing nata. "Momy..." Ya furta a daidai sanda yake shiga cikin ɗakin, ya nemi hanyar kujerar da ta fi kusanci da tata. "Kin kira ni." Ya faɗa yana kallonta da idanuwansa da har yanzu basu gama dawowa daidai ba, ƙwayoyi da cyrup ɗin da ya sha basu sake sa ba. "Ehh. Dadynku ke kiranka." Kanshi ya ɗan sosa kaɗan, cikin daburcewa ya ce, "Momy, lafiya dai ko?" "Ina fa lafiya, Annur? Ka san abin da ya faru kuwa? Ka san muguwar asarar da ka ja wa mahaifinka a kamfaninsa? Wai me yake damunka ne? Sai yaushe zaka san cewa ka girma? Sai yaushe ne zaka kimtsatsa halayenka, su zama na gari, asalin yanda suke a baya?" Shiru ya yi kansa a ƙasa, yana jin haushin kalaman da suke fita daga bakin mamansa, wanda basu da wani tasiri a gare shi. "Da kai fa nake, Annur. Sai yaushe ne zaka zama cikakken mutum mai kamala?" Da ƙyar ya iya ɗaga laɓɓansa ya ce, "Momy ni fa ban san abin da na yi ba." "Ba kuma zaka taɓa sani ba, tun da baka da tunani da lissafin sanin. Ka tashi ka same shi a ɗaki, kai yake ta zaman jira." Tashi ya yi jiki babu ƙwari, a hankali yake ajje takunsa, gabansa na faɗuwa, har ya isa bakin ƙofar ɗakin mahaifinsa. Ba wai baya son shiga ba ne, ba kuma yana tsoronsa ba ne, a'a, kawai dai yana ganin ƙwarjinin Babansa ne, duk iya munanan halayensa yana shakkun Dady. Ba dan komai ba sai irin gatan da yake gwada masa, yake fifita sa a duk cikin yaran da ya haifa, ko da yake dai duk mata ne, shi ne kawai namiji, amma bai kasance mao halayen kirki ba. Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke, kafin a hankali ya fara ƙwanƙwasa ƙofar, ya shiga da sallama ƙunshe a bakinsa. Bai ko amsa sallamar ba mahaifin nasa, ya juyo yana binsa da wani kallo, kallo mai cike da tsantsar takaicinsa da yake ji a daidai wannan lokacin. "Barka da zuwa Dady. Ka kira ni bana nan, ina gidan su Farouk ne. Kuma lokacin magrib ya kusa, shi ya sa kawai na bari har na yi sallah sannan na shigo." Gyaɗa kai kawai Dady ya yi, ba wai dan ya gamsu ba, sai haushinsa kawai da ya ƙara dira a zuciyarsa. "Yanzu Annur abin da zaka min ke nan? Ɓarnar da zaka ma kamfaninmu ke nan? Ni ina ganin na bar komai a hannunka, kana kula da komai yanda ya kamata, ashe banzan tunani nake? Ashe sam! Ba hakan ba ne? Ashe ba zaka taɓa yin abin da zai zama farin ciki a gare ni ba?" Har a lokacin kansa a sunkuye yake, ya gaza faɗin komai, ya kuma kasa haɗa ido da Dady. "Sanadiyyar munanan halayenka, da damar mutane sun fara yunƙurin barin kamfanin, dan babu wani abu da suke ƙaruwa da shi. Ashe kamfanin tractor da suka nemi a masu wasu parts da dama na motocin, har kuɗinsu sun bayar, amma ka saka masu shiririta, ka kasa tsayawa a yi komai yanda ya dace. Dama dai na daɗe da haƙura da zane, tun daga sanda ka warke, ka daina mana zane zane, wanda su ɗin kansu wata asarar ce, tun da inda a ce zaka tsaya ka yi da kanka, na tabbatar za a fi samun yanda ake so, tun da kowa ya sanka, ya san sunanka ta wannan ɓangaren. Amma a karshe dole muka samo wanda yake mana ta wannan ɓangaren, tun buɗe kamfanin bayan warkewarka, kai kuma ka tsaya a naka, general manager. A hakan ma ka kasa yin komai yanda ake so. Ko ka san cewa kuɗin parts of that tractor da suka bayar, sun dulmiye a cikin kamfani, kuma an rasa inda suka shige? Ka san cewa mun yi babbar asara, babu uwar babu ribar? Shi ke nan ai, sai ka zuba ruwa a ƙasa ka sha, ka samu yanda kake so. Ka ga idan kaf ma'aikatan suka gama guduwarsu, sai mu rufe kamfanin, mu ci gaba da zama a haka, tun da abun da kake so ke nan." Ya ƙarisa maganar da ɗaga murya sosai, duk irin ƙaunar da yake gwada wa Annur, amma ya ji ko kaɗan ba zai iya haƙuri ba wannan karon, duk da ya san abubuwan da yake yi a kamfani a baya, bai taɓa tinkararsa da maganar ba sai yau. "Ɓace min daga gani." Ya gwada masa ƙofa da hannuwansa. Da ƙyar ya iya ɗaga tafukan ƙafafuwansa, yana direwa bisa sasanyan tile ɗin da ke baje a farfajiyar ɗakin, da ya ji ƙawa ta ko ina, ga ƙamshi ta ko wane kwararo yana tasowa. *** MARADI, NIJAR. My dearest fans, how are you all? I hope evryone is doing well. You know what? Haka kawai nake ga kaman babu nasara a tattare da wannan plan din na su Maryama, gashi kuma tana neman boye wa mahaifiyarta. Me zaku ce? Shin ya kamata 'ya ta boye wa iyayenta matsalarta, musamman ma uwa mace? Menene zai faru a Maradi, da marubuciyar ke neman mayar da mu can? Sai mu ci gaba da bibiyarta, na tabbatar zata warware mana komai, zamu gamsu da komai a karshe. Thanks all. Ina yinku my fans, irin over din nan, kun sani kuwa? Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:46 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 2⃣9⃣ A tsiyace ya taho da motarsa, wayarsa ce ta yi ƙara a karo na ba adadi, wanda yake ayyana ƙin ɗaukar wayar a cikin zuciyarsa. Wayar na tsinkewa babu jimawa kuma ƙarar text message ya shigo, kamar kar ya buɗe kuma dai ya daure ya buɗe. Abin da ke cikin saƙon wayar ne ya matuƙar razana shi, gabansa ya daɗa dukan uku uku, yana jin yanda zuciyarsa ke tafarfasa, tana tuno masa da mahaifiyarsa. Latsa kiran lambar da ta masa text ɗin ya yi, bai daina zura gudun ba, haka kuma bai ajje hankalinsa sosai ga tuƙin ba, saboda zafin da zuciyarsa ke masa. "A'i, dan Allah ki hwaɗi min Mammata ta samu sauƙi, baninson jin baƙin labarin nan daga gare ki." Cikin muryar kuka wacce ya kira da A'i ta ce, "Shi ke nan Mahmouda, shi ke nan Allah Ya karɓi Mamma, yanzun ga ne likita ya sanar min rasuwarta, dan shi ne ma nake ta kiranka kaƙƙi ka ɗauka, shi ne niyyi maka text ɗin nan." "Innalillahi wa ina ilaihi raji'un!" Ya furta cike da fargaba da damuwa, bai san sanda ya saki wayar ba, gabanshi na tsananta duka, baki ɗaya hankalinsa ya gama tashi. Giccin mutum kawai ya gani a gabansa, da iya ƙarfinsa ya take burki, ya mayar da dukkan hankalinsa ga tuƙin, amma duk da haka sai da ya bugi mutumin, da ƙarfi motar ta tsaya. Dafe kansa ya yi yana tunanin da me zai ji? Zuciyarsa zafi kawai take masa, tashin hankalin da bai taɓa shiga ba yake jinsa a yau. A hankali ya buɗe motar, yana kallon yanda gaban motar tasa duk ya samu matsala, da alama dai wanda ya buga ɗin ya ji jiki. Fatanshi dai Allah ya iyakantar da abun, ya sa ba mai tsawo ba ne. A gaban matashin ya isa, yana kallon yanda matattun kayansa da suka gama jigatuwa da datti jini sai malala yake duk sun ɓaci. Babu ko alamar numfashi a tattare da shi. Duk iya dauriyar Mahmouda sai da ruwan hawaye ya zirara daga idanuwansa, yana jin yanda duniyarsa ta sauya masa a cikin lokaci guda, ya ma rasa yanda zai yi da mutumin da ya buge ɗin. Kafin ka ce kobo wurin ya cika da mutane, wasu na hawaye, wasu kuwa hannuwansu bibbiyu a ka, suna kallon ikon Allah. Wata budurwa ce ta taho goɗoɗo babu hijabi a jikinta, sai wani ɗan ƙaramin mayafi da ta sargafe a wuyanta. Cikakkiyar budurwa ce, mai tsawo da jiki, wacce a shekaru zata iya kai ashirin da biyar ma. Kwanon abinci ne bisa kanta, tana tafe tana rausaya, dukkan gaɓɓan jikinta suna girgiza. Ganin dandazon mutane a bakin titi ya sa ta saki salati, bakinta a buɗe ta tsaya cak tana kallon sarautar Allah. Ita bata matsa inda suke ba, ba kuma ta tafi inda zata je ba. Ganin an cicciɓo wanda aka kaɗe ɗin ya sa ta sakin kwanon da ke bisa kanta, ta ɗora hannunta a ka, da gudu ta ƙarisa inda suke. "Na shiga ukuna ni Fiddou!" Ta faɗa cike da tashin hankali, ta gagara sauke hannunta a ka. "Me ya faru da Modu? Waye ya kaɗe sa? Wayyo niya Allah'na, Modu." Ta sake ɓarkewa da kuka. Ganin kamar Fiddou ta san shi ya sa Mahmouda dakatawa a gabanta, a hankali ya furta mata, "Halan dai kin san shi ne?" Kai ta ɗaga masa cikin kuka ta ce, "Yanzu hakanga abincinshi ne na kawo mai. Amma idona ya gane mini wanga mugun abu. Allah de Ya sa wani abu bai samu Modu ba, wallahi rayuwata zata shiga garari matuƙar Modu ya mutu." Cikin tausayi Mahmouda ya ce, "Ba zai mutu ba giɗe, toho de mu tahi asibiti tare, mu hanzarta tun wani abu bai hwaru ba." Da hanzarinta ta bi bayanshi, gaban motar ta buɗe ta zauna, yayin da aka kwantar da Modu bayan motar, sai wani ɗan unguwar mutum ɗaya a kusa da shi. Sun yi tafiya mai ɗan nisa kafin suka isa wata asibiti wacce da alama ta kuɗi ce. Har ciki suka shiga da motar, da sauri Mahmouda ya kira nurses domin su taho da gado, a bashi taimakon gaggawa idan yana raye. A hanzarce nurses ɗin suka taho da gadon, kafin su iso har wancan mutumin ya fiddo shi, ɗora shi kawai suka yi a kai shi da Mahmouda, sannan nurses ɗin suka tafi accident and emergency da shi. Wani likita mai zafi ya sa aka kira Mahmouda, cikin faɗa yake shaida masa cewa ba zai karɓi Modu ba har sai ya taho da ɗan sanda. Duk irin magiyar da Mahmouda zai ma likitan nan firfir ya ƙi yarda ya karɓe shi, a dole ya hanzarta tafiya Police station tare da wancan dattijon, ya samu ya taho da ƴan sanda mutum biyu, suka dawo asibitin. Suna isowa wayarsa ta fara ruri, da faɗuwar gaba ya ɗauki kiran, muryar ƙanwarsa ya ji ta ce, "Mahmouda ba zaka zo ko jana'izarta a yi da kai ba halan? Walle in dai baka zo ba mun cire ka daga sahun danginmu, mun yafe ka, tun da har ka gagara ka zo ka sallaci mahaifiyarka, dama tun ranta bai fita ba tacce a kirawo ka kui bankwana, babu irin kiran da ban yi ma ba amma kaƙƙi zuwa, daga ƙarshe ma sai kab bar ɗaukar kiran nawa, har Allah Ya karɓi rayuwarta, kuma bayan mutuwar tata ma ka ƙi zuwa. Babu komi Mahmouda, mun gode." Kawai ta tsinke wayar da wani irin kuka. Dafe kansa ya yi, wayar tasa ma sakinta ya yi ƙasa, yana jin yanda zuciyarsa ta masa nauyi sosai, kamar ba zata iya ɗaukar baƙin cikin da yake ƙunsa mata ba. "Ka yi shiru giɗe, ka biya kuɗi ko ana samu a ceto rayuwar wancan bawan Allah tun bai mace ba." Masifaffen likitan ya faɗa a karo na uku da yake ma Mahmouda magana bai ma san yana yi ba. "Ina zan je in biya halan?" Ya samu da ƙyar ya fiddo maganar, bayan ƴan daƙiƙu da ya yi shiru yana sauraren likitan. "Tahi can, zaka ga hanyar Pharmacy ceniya, ka tai can ka biya kuɗɗi, zasu baka rasiɗi sai ka kawo can a cike masa katinsa, sannan ko ina duba shi." Tafiya ya yi inda likitan ya kwatanta masa, bayan ya biya kuɗin ya dawo medical record, ya basu reciept sannan aka cike masa katinsa. A wurin suna sai da ya tambayi Fiddou, ta ce kawai a saka masa Modu Najibou, sannan aka miƙa katin ofishin likita, aka tafi da Modu da har yanzu ko motsi baya yi. A cikin zuciyar Mahmouda kuwa tir kawai yake da hali irin na wannan likitan, ko kaɗan bashi da kirki bare ya roƙi alfarmar tafiya wurin jana'izar mahaifiyarsa. Ganin kaMar akwai sassauci a fuskar Ƴan sandan ya sa ya faƊa masu komai, a ƙarshe ya nemi alfarmar zai je ya halarci jana'izar mamansa da ta rasu. Daga farko basu amince ba, sai daga baya suka tausaya masa, suka yanke hukuncin ɗaya daga cikinsu zai bi Mahmouda, idan an gama su dawo tare, har sai an ga yanda hali ya nuna ga wanda aka kaɗe ɗin. Sefa ya zaro daga aljihunsa wanda bai ko tsaya ƙirgawa ba, a hankali ya tako har inda Fiddou take, yana kallon yanda idanuwanta ke zubda ƙwalla, wanda hakan ya tabbatar masa da cewa lallai wannan mutumin da ya banke yana da matuƙar muhimmanci a rayuwar Fiddou, musamman ma da ya ga zallar tashin hankali a cikin ƙwayar idonta. Kuɗin ya miƙa mata, fuskarsa babu walwala ko kaɗan a tattare da ita. "Mi zan yi da su halan?" Ta jefo masa tambaya ba tare da ta karɓi kuɗin ba. "Zan tai in dawo, Mammata ta rasu za a yi jana'izarta yanzu, shi ne zan tai, kuɗin ga kuma ko akwai abin da za a buƙata nashi kahin in dawo." Jiki babu ƙwari ta ɗaga hannuwanta da take jin sun mata nauyi ƙwarai ta karɓi kuɗin, ba tare da ko kallonshi ta yi ba. Saboda a zahirin gaskiya wata irin tsanarshi take ji a zuciyarta, a ganinta kaman duk abin da ya faru da Modu SHI NE SILA, dan haka bata jin akwai sauran wani abu da zai yi ya burge ta. "Allah Ya bashi lahiya, sai na dawo giɗe." Bata ce masa ko uffan ba, haka kuma bata sake kallonsa ba har ya ɓace ma ganinta, ta sake fashewa da wani kukan. Tana nan zaune a reception ta ji muryar waccan nurse ɗin tana mata magana, "Giɗe kin taho nan kin yi zaune, mi da baki matsa inda likita ba halan? Giɗe ya tashi kuma bai san kowa ba. Gashi can likita ya gama kula da shi har ma an kai shi ɗakin maza an kwantarshi." Tashi Fiddou ta yi a saɓule ta share hawayenta, duk irin rashin natsuwa na Fiddou amma ta koma kamar ba ita ba, tafiya ma a hankali take yinta, haka magana ma a natse kamar dai ba ita ba. "Wane ne ɗakinsa halan giɗe?" "Mu tai in kai ki." Bin bayan nurse ɗin ta yi shima ɗayan ɗan sandan ya bi su, suna isa male ward ta ce, "Ku shiga, gadon da zai kallo ku shi ne an na giɗe." Shiga ciki suka yi bayan nurse ɗin ta tafi. Tun daga nesa ta hango shi an maƙala masa ledar jini, da alama jininsa ya fita sosai, dama kuma bata yi mamaki ba, la'akari da yanda kayanshi suka yi kace kace da jini, kamar an yanka wata dabba an goge da kayan nashi. Da kuka ta ƙarisa zama kusa da shi, tana gyaɗa kai tana faɗin, "Sannu Modu, sannu sannu. Wallahi laihina ne duka wanga, laihina ne da ban zo na kawo ma abinci da wuri ba, na san yunwa ce ta ishe ka ka nemi ƙetaro titi ka biɗo ni, shine wagga ta'asa ta hwaru. Allah Ya baka lahiya Modu." A hankali ya fara buɗe idanuwan nasa, da ƙarfi ya ƙarisa buɗe su, yana tunanin a inda yake, da kuma halin da yake ciki. "Modu..." Ta faɗa da murmushi mai haɗe da ruwan hawaye. Murmushi shi ɗin ma sakar mata, kafin ya fara yunƙurin tashi zaune. Miƙewa ta yi da sauri ta ce, "A'a hwa Modu, halan baka ga baka da lahiya ba? Koma ka kwanta ka jiya? Ka natsu dan Allah dai." Bai koma ya kwanta ɗin ba sai kallonta da yake yana murmushi irin na taɓaɓɓi , yana ɗan zaro idanuwansa. "Walle giɗe ina hwasawa, ina hwasa kai ka inda take." Yana jin ta faɗi haka ya koma ya kwanta, yana ɗan gyaɗa mata fuska alamar kar ta fasa, ruwan hawaye na zirara daga idanuwansa, murmushin da yake kuma bai kau ba. "Yauwa ko kai hwa. Ka bari har likita ya gama duba ka sannan ko mi zaka yi sai ka yi abinka. Ka ga yanzu baka da lahiya ne, jininka ya fita sosai sai da aka siya wani shi ne ake ƙara ma." Murmushin fuskarsa ya faɗaɗa, bai ɗauke kallonsa daga Fiddou ba ya ce, "Ni bani son wannan jinin, ku bar ni da nawa wanda ke gudanya da..." Bai ƙarisa maganar ba ta kalle shi ta ɓata fuska, "Wai Modu me yake damunka ne? Na hwaɗi ma jininka ya hita da yawa hwa, mi da ba zaka yi shiru hakan nan ba halan?" Shirun kuwa ya yi ganin kamar ranta ya ɓaci. Ya runtse idanuwansa alamun baccin ƙarya yake, sai kyarma idanuwan ke yi, hawaye kuma bai daina fita daga cikinsu ba. Suna cikin haka sai ga wata nurse ɗin ta daban ta zo, hannunta riƙe da kwando mai ƙunshe da allurai da magunguna. "Giɗe hala wanga ne Modu?" Ta ce da Fiddou tana kallonta. Kai kawai ta ɗaga mata. Matsawa ta yi inda yake, tana yi tana magana, "Hala har yanzu bai hwarka ba?" "Ido nai biyu ai ko yanzu. Modu!" Ta kira sunansa yanda zai ji. Idonsa guda ɗaya kawai ya buɗe, shi ɗin ma ba duka ba, ya ɗan ƙwanyarasa a fuskar Fiddou kaɗan, sannan ya sake rufewa yana murmushi. "Modu likita ta hwa zata baka magani. Mi da kake satar kallo na halan?" Dariya ta so ta ɗan ƙwace wa nurse ɗin da kuma wancan ɗan sandan da ke tsaye yana kallonsu. Yanayin na su Fiddou akwai ban dariya. Allura ta haɗa nurse ɗin kafin ta fara tunanin ta yanda zata fara, dan ta ga alamar taɓaɓɓe ne ba kansa ɗaya ba. "Giɗe halan ya zan yi da wannan Modu?" Ta juyo ga Fiddou tana tambayarta. "Kuma walle Modu bashi son allura. Akwai sanda yai yi wani ciwo an sha daga da shi kahin a yi allurar nan. Amma na san yanda zan yi da shi." Ta faɗa haɗe da mayar da kallonta ga Modu da murmushi. "Modu ka ƙi buɗe idanuwanka ko? Walle idan baka buɗe su ba ba zan kai ka inda take ba, sai dai ko kukan jini zaka yi ka yi." Da saurinsa ya buɗe idanuwan yana ware su a kanta, ya washe baki wanda dariyarsa kawai zaka kalla ta tabbatar maka cewa mahaukaci ne. Banda ƙazantar da ke jikin tufafinsa, da kuma sumar da ta gama mamaye kaf ilahirin fuskarsa, ta bisa kai kuwa dama ta yi tsawo har ta gaji, da alama dai ya jima bai yi aski ba. "Mi zan yi ya yarda a yi?" Nurse ɗin ta faɗa a tsorace, dan bata so wani abu ya same ta, kuma da alama dai baya son allurar, dan yanda ta ga yana binta da kallo ita da allurar tata, gudunta ma kar ya mammake ta. Magana ta mata ƙasa ƙasa yanda Modu ba zai ji ba, kafin a hankali Nurse ta murmusa, ta kalli Modu ta ce, "Kana so na kai ka wurin Amrah?" Da sauri ya fizge ƙarin jinin da ake masa, ya diro daga bisa gadon, duk da ciwukan da ke jikinsa basu hana shi kuzari ba, yana kuka yana dariya da furucin, "Dan Allah ki kai ni wurinta, wallahi *AMRAH NAKE SO!"* How are y'all? I hope y're all fine. How was this chapter? Kun ji ta daban ko? Ina fatan dai kuna gane maganar ta 'yan Nijar...lol😁 What do you expect? Who is that mahaukaci mai fadin AMRAH NAKE SO? I think he is the lover of Amrah, irin sosai da sosai din nan. Which Amrah? The writer of AMRAH NAKE SO? No. Her namesy from HOUSE OF NOVELS? I don't think so. To wace Amrah ce wannan? Ba dai wacce ta mutu ba ko?😳 Na hakura da jero expectations din nan nawa dai. Na bar ma marubuciyar ta warware min komai. Da haka nake son kuma masu karatu ku bar marubuciyar, ita zata bayyana maku komai. Many regards to the readers of this book, especially those that reads and votes, not the ghosts, ehen🙄 Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:47 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 3⃣0⃣ Saurin dakatar da shi ta yi da faɗin, "Koma ka kwanta in dai kana so na kai ka wurin Amrah. Ka kuma natsu na maka allurag ga ko kuma in hwasa." Duk da baya son allurar amma a haka ya haƙura ya koma bisa gadon ya kwanta. Jikinsa sai karkarwa yake har ta samu da hikima ta soka masa allurar, tana yi tana faɗin, "In dai yana son zuwa wurin masoyiyarsa Amrah to bana so ko motsi ya yi har sai na ƙare yin alluragga." Da haka har ta samu da zare allurar daga jikinsa. Tana gamawa kuwa ya fara ƙoƙarin saukowa daga bisa gadon, fuskarsa da murmushi yana faɗin, "Ki kai ni wurinta. Dan Allah ki kai ni na ga Amrata." Rasa yanda zata yi da shi ta yi. Kwandon ta ɗauka ta yi tsaye tana tunanin mafita. Jin muryar Fiddou ta yi ta ce, "Sai ka yi bacci ka tashi sannan zata kai ka. Yanzu ka kwanta ka huta kahin a jima." Komawar kuwa ya yi ya kwanta, yana wani irin yaƙe, haƙoransa da suka gama rinewa suka bayyana. Gyaɗa kai kawai nurse ta yi cike da tausayi ta bar wurin. Dama allurar da ta masa har da ta bacci ta zuba a ciki. Take bacci ya ɗauke sa sai sauke ajiyar zuciya yake. KATSINA, NIGERIA. "Maryama, wato dai ba zaki faɗa min damuwarki ba ko? Yanzu kina ga kaman kina da wacce ta fi ni ne? Kina da wacce zaki tinkara da damuwarki wadda ta fi ni? Idan na shiga wata damuwa, zaki ji daɗi ki tambaye ni matsala ta na ƙi faɗa miki? Haba Maryama! Ya kamata fa ki san ke ba yarinya ba ce, kin wuce lokacin da zaki ringa ɓoye min damuwarki. Aikin Muhammad ne wannan ba naki ba Maryama." Ajiyar zucuya Maryama ta sauke. Tana tunanin ta faɗa mata gaskiya ko kuwa dai kawai ta faɗa mata yanda suka yi da Jiddah? Shawara ta yanke kawai cewa kar ta faɗa mata gaskiya, saboda abin da Jiddah ta faɗa tsaf zai iya faruwa. "Mama, na samu labarin wata baiwar Allah ne, labarin da ya matuƙar razana ni, ya zauna min a zuciya, nake jin tausayin baiwar Allah'r har cikin zuciyata." Cikin matsuwa da son jin zancen Mama ta ce, "Ehen, mabuƙata ne, a taimaka masu?" "Ko kaɗan Mama, ba haka ba ne. Amrah ce..." Ta kwashe komai ta faɗa wa Mama, sai dai ta ɓoye mata taimakon Annur da take son yi. Zafafan hawaye ne suka ringa fita daga ƙwayar idon Mama. Tana jin yanda tausayin Amrah ke ratsa duk ilahirin zuciyarta. Take jin tsananin bugawa da zuciyarta ke yi. Wace irin yarinya ce wannan? Wace irin mace ce mai tattare da halayen kirki? Dama akwai irinta a wanann zamanin? Ashe akwai masu kyawawan hali irin Amrah? "Wannan ita ce damuwata Mama. Dalilin da ya sa kika gan ni cikin damuwa ke nan. Na rasa yanda zan yi da tausayin Amrah. Rayuwarta da mutuwarta duka abin tausayi ne. Akwai manyan darussa a cikin labarin Amrah, wanda saurarensu kawai wani babban ilimi ne." "Dole ne zaki shiga damuwa Maryama. Dole hankalinki ya tashi. Ina miki fatan kasancewa da irin halayen Amrah, ko da ba duka ba. Idan har kika kasance haka kuwa zan daɗa alfahari da ke, zan ninka gatan da nake gwada miki, zan ci gaba da tutiya da ke a duk inda zan shiga." Rungumar Mamanta ta yi, cikin kuka ta ce, "Ina alfahari da ke Mamana. Insha Allahu zan ci gaba da kwatanta halayen Amrah. Zan zamto abar alfahari a gare ki, kamar yanda Maman Amrah ke alfahari da Amrah, tun tana raye har bayan mutuwarta." Murmushi Mama ta saki a fuskarta, tana jin yanda soyayyar ƴarta ke shiga a duk gaɓoɓinta, ƙaunarta take ji ta ko wane saƙo na zuciyarta. Suna cikin haka Muhammad ya shigo, School bag ɗinsa ya jefar a ƙasa yana mai ƙirƙiro kuka ya ce, "Mama yau ma..." Bai ƙarisa ba Maryama ta dafe kanta haɗe da faɗin, "Problem boy. Yau ma me?" "Yaya Maryama ban fa yi masa komai ba ya daken." Ya faɗa fuskarsa a daƙune, kamar ta ce zata masa wani abu ne. "Kullum haka kake fa Muhammad. Ban san me ya sa ba sam ba ka ci sunan nan ba. Asalin mai sunan haƙurarren bawa ne, mai kyawawan halaye. Amma kai kam ko kwatantawa ma baka yi, na rasa dalili." Zama ya yi a bakin gado bakinsa tunzure yana faɗin, "Ai dama Yaya Maryama ban taɓa ji kin yabe ni ba, komai sai dai ki ce bani da gaskiya." Dafa kafaɗarsa ta yi murmushi ƙunshe a fuskarta ta ce, "Amma ai ka san bani da kamarka ko? To duk abin da zaka ga ina maka ƙauna ce ta ja haka. Ko so kake kawai ko yaushe na yita goyon bayanka, bayan kuma ba gaskiya ba ne?" Janye hannunta ya yi daga kafaɗarsa ya ce, "Ni dai ban yarda ba. Daga ke har Mama da Abba kuna nuna min banbanci. Ko kaɗan bakwa gwada min soyayyar da ta dace." Zaro idanuwanta ta yi cike da mamakin kalaman fa suke fitowa daga bakin Muhammad, "Wace irin magana ce kake haka, Muhammad? Kana da hankali kuwa?" Tashi Mama ta yi ta gyaɗa kanta, ta kalli Maryama da faɗin, "Ki fahimtar da shi Maryama. Na kula dai wani abu ne ya ɓata masa rai tun asali. Idan kun gama ki rako shi akwai kyautar da na ajje masa ta musamman." Murmushi ta saki Maryama, ta ce, "Mama zaki bar ni da rigimammen yaron nan ke nan. Iyaka na zazzane yaro idan zai min shegantaka." A daidai fitar Mama ta ce, "Kun fi kusa ai." Ta ƙarisa ficewa daga ɗakin. Juyowa ta yi ga Muhammad da fara'a ta ce, "In banda abunka Muhammad, kai kaɗai ke nan namiji a gidan nan, ta ya kake tunanin ba zamu ƙaunace ka ba? Duk abin da ka ga muna maka fa muna son ka kasance na gari ne. Ko hausawa sun ce ka so naka duniya ta ƙi sa, ka ƙi naka kuma duniya ta so shi. Idan muka bayyana soyayyarmu a gare ka, baka tsammanin wani abu zai je ya dawo? Abin da mutanen yanzu suka kasa fahimta kenan. Yana ɗaya daga cikin abubuwan da suke taɓarɓarar da tarbiyyar yaran zamani, wato nuna masu soyayya da gata, a kasa nusar da su abin da ya dace da su. Komai suka kawo kawai daidai ne. Muhammad so kake ka zama sangartaccen yaro?" Sai a sannan ya fara saukowa, cikin sanyin murya ya ce, "Amma Yaya Maryama ko yau fa mantawa aka yi da ni a makaranta, ba a je an ɗauko ni ba. Kuma na shigo gida, baku damu da sanin wa ya kawo ni gida ba. Duk ƙaunar ce wannan?" Dafe kai ta yi Maryama, tana jin haushin kanta na mantawa da ɗauko Muhammad da suka yi. Sai yanzu ta tuna Abba ya kirata a waya ya sanar mata ba zai samu ɗauko Muhammad ɗin ba, kuma drebansa ya tafi ƙauyensu yau. Cike da damuwa ta ce, "Yi haƙuri Hammad ɗina, ko kaɗan kar ka ga laifin Abba da Mama. Laifin nawa ne, saboda Abba ya sanar min na biya na ɗauko ka idan na tashi, sai kuma na ji bana jin daɗi ban je lecture ɗin ba. Ka gafarta min ka ji ƙanina?" Da dan murmushi shimfiɗe a saman fuskarsa ya ce, "Babu komai, Yaya Maryama komai ya wuce." "Yauwa ƙanina abin alfaharina. To ya aka yi ka dawo? Ka hawo mashin ne?" Bayan ya miƙe tsaye yana ƙoƙarin cire neck tie ɗin uniform ɗinsa ya ce, "Maman Abdul ce ta ɗauko mu tare, ita ta kawo ni har gida." Miƙewar ita ma ta yi Maryama, ta ce, "Wacece kuma Maman Abdul? Ban taɓa jin sunan a bakinka ba." "Wani yaro ne ɗan Nursery 2. Yana yawan zuwa wurin abokina Khalid ne, a nan na san shi har muka shaƙu. Muna mutunci sosai da yaron. To dama wani lokaci idan mamanshi ta zo ɗaukarsa kafin a zo ɗaukana ina zuwa in gaishe ta, har ta ce zata tafi da ni, ni kuma sai in faɗa mata za a zo a ɗauke ni. To yau kuma sai bata zo ɗaukarsa da wuri ba, ni ɗin ma kuma haka. Muna ta jira sai gata ta zo, ganin duk ɗalibai sun watse ya sa ta ce kawai na zo mu tafi ta sauke ni. Dalilin da ya sa bata je ɗaukarsa ba wai ta shiga yin surgery ne, da yake likita ce. Har ma ta ce min zata zo har gida ta gaishe da Mamana, saboda yanda nake kula da yaronta." Jinjina kai Maryama ta yi, ta ce, "Ka dai ringa kula sosai da irin wannan abubuwan. Yaushe ta ce zata zo?" "Ni dai ta ce min wai zuwa anjima zasu zo, tun da dai ta ga gidan yanzu." "To shi ke nan, Allah Ya kawo ta lafiya." Daga nan ta fice daga ɗakin ta koma falo. *** Zaune yake ya zabga uban tagumi, kwalaben syrup ne jere a gabansa, ga wata irin sigari babba, irin marar warin nan da turawa suka fi amfani da ita. Damuwa ce shimfiɗe cikin zuciyarsa, wanda har fuskarsa ta gagara ɓoye hakan. Bai ko tsaya yin diluting ba, kwalbar kawai ya ɗaga ya kai bakinsa, bai sauke ba har sai da ya shanye tas, ko ɗis bai rage ba. Ajje kwalbar ya yi sannan ya kai sigarin a bakinsa, yana yi yana gyaɗa fuskarsa, cike da ƙunci da baƙin ciki. "Kar dai maganar boka ce ke neman tabbata. True love ɗin da na faɗa ne ke neman kawo min cikas ko kuwa? Ta ya Dady da kansa zai hau ni da faɗa, saboda abin da ba yau aka fara yinsa ba? Yau na fara jawo hasara a kamfani? Akwai matsala!" Ya sake fasa wata kwalbar syrup ɗin ya kaita bakinsa. Bayan ya shanye duka ya ajje, yana neman kai sigari a bakinsa ya ji wayarsa na ƙara. Ɗauka ya yi ya kara a kunne, cikin muryarsa da ta fara canzawa ya ce, "Hello babe!" A ɗayan ɓangaren aka amsa da, "Akwai damuwa my A. Babu kuɗi hannuna kuma ina da matsaloli da dama. Ya za a yi?" Wata budurwa ce ta yi maganar, wacce yanayin maganarta kawai zai tabbatar wa mutum cewa ita ɗin ma irinsa ce. "Babe ya kike so a yi?" Ya furta yana lumshe idanuwansa. "My A. ka turo min kawai, ko akwai matsala ne?" Canza wa wayar muhalli ya yi, daga gefen hagu ya mayar gefen dama, ya matse ta da kafaɗarsa sannan ya ƙoƙarta da hannun da sigarin take ya buɗe wata kwalbar syrup ɗin. "My A. Na ji ka yi shiru, da alama dai akwai damuwa." "Babu damuwar komai. Ina up ne." Dariya ta tulle da ita kafin ta ce, "Har ma sai ka faɗa? Voice ɗinka kawai ya tabbatar min da hakan." "Na sani ai. Ina zamu haɗu?" Sai da ta ɗan yi shiru kaɗan, kafin ta ce, "Dole sai mun haɗu zaka bani? Me zai hana ka min mobile transfer kawai?" Cikin yanayin slow ya ce, "Da wasa kike babe, kin san bana fitar da kuɗina a haka nan. Dole na fanshe a jikinki." "Amma my A. Na ga ka hau up da yawa, ba zaka iya yin komai ba. Gashi kuma ni a matse nake da kuɗin, zamu je wani biki ne Maraɗi. Gobe da sassafe zamu tafi." Cikin halin ko in kula ya ce, "Zan miki transfer na 50k yanzu. Amma ki sani, zan fanshe ko ba yanzu ba." "Babu komai." Ta faɗa haɗe da tsinke wayar tana dariya. Yana kashewa ya yi searching account number ɗinta, ya tura mata kuɗin. Shi kuma ya ci gaba da shan kayan mayensa, wanda suka mantar da shi duk damuwar da yake ciki, damuwar da dady'nsa ya saka shi. Me zaku iya cewa masu karatu? Shin kun hango wani abu a cikin chapter'n nan kuwa? Idan kun hango, menene? Feel free and tell me your expectation. Ni dai na ce bana tunanin komai, what of you? Na gode kwarai da addu'o'inku. Alhamdulillah! Na ji sauki sosai. Mura dai ce har yanzu voice dina ya gagara komawa daidai. Ku ci gaba da yi min addu'a, ina matukar jin dadin hakan. Na kokarta yi maku 2k words duk da rashin jin dadin jikina. Don farin cikinku kawai masoyana. Basman mai sanyinta ina yinki over, ina farin cikin kasancewarki a duniyata, ke din ta daban ce, ba zan gajiya da yi miki fatan alkhairi ba. Aunty Maijidda Musa kina ina? Hakkun kina faranta min rai. Amrah na kaunarki irin totally din nan, fatan kin san da hakan. RAZ NOVELLA 1&2 Ina kaunarku fi sabilillah! Kaunar taku a jinin jikina take, ina alfahari da ku, ina kuma yaba maku da comments a kan wannan littafin. Hakan na dad'a kara min kwarin guiwa sosai da sosai. Kun san ina kaunarku kuwa? Sauran groups da nake ciki duk ina yinku. Ina matukar kaunarku, ina jin dadin kokarinku na yada wannan littafin har ya zagaya inda ban taba tsammani ba. My dear Kdeey kaunarki a kahon zuciyana take, kin sani kuwa? Kar dai na cika ku da surutu, sai mun hadu a next page idan Rabbissamawati wal'ard ya nuna mana. Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:47 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 31 Buɗe idanuwansa ya yi ya sauke su a bisa fuskar Fiddou da ta tsura masa nata idanuwan tana kallonsa ko ƙaƙƙautawa babu. Da ƙarfi ya fizge ƙarin ruwan da aka dasa masa yanzu, babu wata wata ya diro daga bisa gadon, yana kallon Fiddou da murmushi a saman ƙazamtacciyar fuskarsa mai cike da suma babu kyawun gani. Murmushin yaƙe ta mayar masa, tana ƙoƙarin miƙewa tsaye da faɗin, "Ina zaka tai ne Modu? Giɗe koma ka kwanta do Allah de." Kai ya gyaɗa mata alamar ba zai koma ba yana ƙoƙarin ci gaba da tafiya da ɗangyasasshiyar ƙafarsa, ƙafar wandonsa ɗaya ta gama yayyagewa, tun daga ƙasa har kusan rabin wandon. Saurin shan gabansa ta yi tana faɗin, "Modu walle in dai kattai ba zan kai ka inda Amrah ba. Idan kuma baka so in kai ka ton ka tahi." Duƙewa ya yi a daidai inda yake, ya saki kuka da sauti mai ƙarfi, wanda ya karaɗe asibitin, yana bada wani echo sound har inda babu mutane yana amsawa. A rikice ta duƙa ita ma, ganin halin da yake ciki ba ƙaramin firgita ta ya yi ba, a tunaninta ko wani abun ne na daban ya same sa. Mutane ne da dama suka tasan ma ɗakin, ganin mahaukaci a duƙe yana rizgar kuka ya razana su sosai. Suka ringa bin Modu da Fiddou da kallon mamaki. "Modu da Allah dai ka hwaɗi min abin da akka damunka. Halan wani abu ke maka ciwo?" "Ba ke ce kike min ƙarya ba? Kullum kina cewa zaki kai ni wurin masoyiyata Amrah amma kina ƙin kai ni. Ni idan baki kai ni ba zan guduwata ne daga asibitin nan, kuma ba zaki sake ganina ba." Cikin tashin hankali Fiddou ta ce, "Na shiga ukuna ni Fiddousi! Modu ina zaka tai ka barni? Ko son kake yi in shiga tashin hankali?" Banza ya mata yana mai ci gaba da kukansa, sai dai yanzu ya rage sautin kukan nasa. Ɗaya daga cikin mutanen da suka zagaye su ne wani ya tako har inda suke, da alama yana jinyar wani ne a wani ɗakin na daban. A hankali ya dire ƙafarsa a gaban su Modu, ya sunkuya a saitin fuskarsa, da murmushi ya ce, "Haba abokina! Ya zaka ringa abu kaman ba jarumin maza ba?" Ɗago kansa Modu ya yi, ya daƙune fuska yana kallon mutumen, a hankali da wata murya kamar mai hankali ya ce, "Ni ba jarumi ba ne." Dariya suka ɗauka su duka ɗakin, har Fiddou sai da maganar tasa ta so ta saka ta dariya, sai dai ta danne, sanin cewa Modu baya son dariya ko kaɗan. Wani kukan ya sake fasawa, kamar ma ya fi wancan na farkon ƙara. "Ni kuke wa kuka? Ki faɗa masu fa bana so ana min kuka, yanzu zan daki yara, to ni dai na faɗa maku." Yana faɗin haka kuma ya miƙe tsaye yana murmushi, kamar ba shi ne ya gama hayagaga a ɗakin ba. "Wai dan ƙarya suka ce Amrah ta mutu. Ni na san Amrah ba zata taɓa mutuwa ta barni ba. Rayuwarta don ni aka yi ta, ni kaɗai. Ban san inda take ba da na gano ta. Na san ita ɗin ma tana can tana jira na, in je mu yi aureee." Ya ƙarisa maganar da janta yana murmusawa sosai. Yana gama faɗin haka ya fara dafe kansa, jiri na ɗibarsa, ya faɗi ƙasa luuu haɗe da sakin kan nasa. Ba Fiddou kawai ba, har sauran mutanen wurin sai da hankalinsu ya tashi. Da sauri suka yo kansa, wasu na bubbuga shi a hankali ko zai tashi. A rikice Fiddou ta nufi nurses station ta kira nurse ɗin da ta karɓi evening, a hanyar dawowarta ne ta haɗu da Mahmouda da wasu ƴan mata guda biyu zasu je ɗakin Modu, sai kuma wannan ɗan sandan guda ɗaya biye da su. Cikin sakin fuska Mahmouda ya ce, "Fiddou a gaishe ki." "Iyi giɗe. Shine kat tahi ka ƙyale mu ko? Tun jiya nit ta tunanin dawowarka amma na ji ku shiru." "Giɗe ke san na hwaɗa miki Mammata ta rasu, jana'izarta ce ma nittai. Dan shi ne ban samu na dawo jiyan ba. Bawan Allah'nga ma shaidana ne. Na so dawowa to kuma sai mutane sunkai ta zuwa wurin gaisuwa. Ga ƙannena nan guda biyu ma nit taho da su." Da murmushi ta kalli daka dakan ƙannen nasa, wanda duk girman jikinta sun ce mata kau ban wuri. "Giɗe mun same ku lahiya? Ya me jiki?" Ɗaya daga cikin ƴan matan ta faɗa da fara'arta. "Ina hwa lahiya ga giɗe can ya hwaɗi ƙasa, dan shi ne ma nik kirayi giɗen ceniya da ta shiga ɗaki yanzu." Da damuwa Mahmouda ya ƙara takunsa har ya isa cikin ɗakin, fuskarsa na nuna zallar tashin hankalin da yake ciki. Bin bayansa suka yi su duka, har ɗayan ɗan sandan da yake biye da su ƙiƙam, kamar suna masa jagoranci. Ko da ya je har an cicciɓi Modu an dirar bisa gadonshi, Sister kuma ta koma ta kira likita ta dawo, dan a yanda mutanen wurin suka faɗa mata matsalarsa kamar abun ya fi ƙarfinta. Dafa kan Modu ya yi Mahmouda, cikin tausayi ya ce, "Yi haƙuri Modu, ni ne sila, ni ne najja maka wagga wahala da kake cikinta. Damuwar da nake cikinta tassa na kasa controlling temper ɗina, har sai da nik kaɗe ka ban sani ba. Do Allah de ka yahe man." Ko motsi Modu bai yi ba bare Mahmouda ya sa ran zai farka, ko kuma yana jinsa. Suna cikin haka ne likita ya iso da nurse biye da shi. Hakan ya sa sauran nutanen da ke ciki duk suka watse, har su Fiddou ma a bakin ƙofa suka dakata. Dudduba shi likita ya yi sosai kafin ya ce, "Ina ga kamar akwai wata asalin damuwa ne a cikin zuciya tai. Ba wai bankar da mota tai yi mai ce kawai matsala tai ba. Kuma matsalad da ac cikin zuciyatai bata rasa nasaba da taɓin ƙwalwar da garai. Dole sai na ji daga bakin wani nashi ko ina sanin abin da ka hwaruwa da shi." Cikin gamsuwa da girmamawa nurse ɗin ta ce, "Bari in kira wacceni da suke tare." Ta kama hanyar ƙofa, ta ci burki a inda su Fiddou suke, ta sanar mata cewa likita na son ganinta. Tare suka tafi wurin likitan, ita da nurse. "Giɗe halan ya kuke da Modu?" Muryar likitan ta daki kunnuwanta tun bata ƙarisa isa kusa da gadon ba. Shiru ta ɗan yi na wani lokaci tana nazarin abin da zata faɗi. Jin babu amsa ya sa likitan ci gaba da maganarsa, "Ke ga ga abun gwajin zuciya nan, da shi na auna nagga yanda zuciyatai bata tahiya daidai yanda aka son ta yi. Kuma wannan matsala ko kaɗan bata da alaƙa da wanga kaɗe shi da giɗe ya yi da mota. Sai na tabbatar da komai kafin in san matakin da zan ɗaukar mai, idan ma likitan zuciya ya kamata in haɗa ku da shi sai in hwaɗi mai." A yanzun ma shiru ta yi dan bata san ta inda zata fara ba. Tsayuwar ta yi yawa ya sa likitan cewa, "Giɗe biyo ni Office mu yi magana. Ba maganar a tsaya a yi nan ce ba. Ina son taimakon giɗe, wata ƙila idan na san komai har likitan ƙwalwa sai a haɗa ku. Amma hwa yanzu dole a tari matsalar zuciyag ga tun abu bai yi nisa ba." Yana direwa ya fara takawa zuwa hanyar fita. Ita ma Fiddou binsa baya ta yi. Har ya yi nisa kuma ya juyo ga nurse ya ce, "A kuka da shi sosai hwa. Kar ki bar wuringa dan kar ya hwarka babu kowa a tattare da shi. Tun da na hidda kowa daga ɗakin, na kuma hana su shigowa. Matsalar da ta shafi zuciya hwa dole sai ana taka-tsantsan." Fita suka yi tare da Fiddou suka nufi Office ɗinsa. A zuciyarta tunanin yanda zata yi da likitan kawai take. Bata san ta yanda zata fara faɗa masa a haka ta ganshi har suka shaƙu ba. *** Da gudunshi ya shigo yana faɗin, "Yaya Maryama! Yaya Maryama!!" Ɗago kanta ta yi daga latsar wayar da take da sauri tana binsa da kallon tuhuma, tuhumar dalilin shigowarsa ɗakin babu ko sallama kuma sai ihu yake mata. Raina kansa ya yi ganin kallon da take binsa da shi. "Uhmm...dama, dama Maman Abdul ce ta zo. Tana falo Mama ta ce na kira ki." Fasa yi masa faɗan da ta yi niyyar yi ta yi, gyaɗa kanta kawai ta yi ta ajje wayar bisa gado, sannan ta zira hijabinta iya guiwa, ta nufi hanyar falon. Ko da ta isa ta samu Mama suna fira da Maman Abdul, firar abun da ya faru ɗazu, na rashin zuwa ɗauko sa. Da fara'a Maryama ta zauna, gaishe da Maman Abdul ta yi sannan ta miƙe ta nufi kitchen. Fruits ta yayyanka cikin lokaci ƙanƙani ta haɗa ftuit salad ta fasa ƙanƙara ta ɗora a kai. A bowl ta juye ta haɗa da cokali sannan ta koma falon ta ajje a gaban Maman Abdul da faɗin, "Ɗazun nan kuwa Muhammad ke ce min wai ya ji ku shiru har yanzu, gashi kuma babu lambarki bare na kira ko kun fasa zuwa ne." Cokali guda ta kai bakinta sannan ta ajje ƙasa, ta dubi Muhammad da fara'a ta ce, "Abdul ne zai ƙyale ni bamu zo ba? Ai yanda ya saka ka a ranshi abun ba a magana. Kullum damun Abbansa yake da maganarka. Abban nasa ma ya tilasta lallai kar mu wuce yau bamu zo gidanku ba." Mama ta ce, "Yara kuwa sun haɗa zumunci." Ta faɗaɗa murmushinta. Sun jima suna hira har magrib ta kusa. Muhammad da Abdul kuma suna harabar gida suna buga ƙwallo. Miƙewa ta yi ta ce, "Bari dai mu kama hanyar gida Mama. Maryam mu yi musayar number mana." Miƙewa ta yi ita ma Maryama ta ce, "Aikam mu ma insha Allahu muna nan zuwa gobe ko jibi. Zamu zo mu ga gidan su Abdul daga nan sai zumunci." "Da kuwa na ji daɗi ƙwarai." Suka yi musayar lambobin wayar sannan Maryama ta taka mata har tsakar gida. Ta ce, "Maman abdul baki faɗa mana sunanki ba." "Dr. Islam sunana." Daga nan suka isa tsakar gidan. "To malami sai a zo mu tafi ko?" "Oh Mami! Muna kan yin ball ne zaki ce mu tafi?" Ya faɗa cikin shagwaɓa da yarinta. Duka a shekaru ba zai wuce shekara uku ba, ba ma lallai idan zai yi ukun ba. Amma sai wayo da son mutane yaron. "Abdul-Ahad dare ya yi fa. Ko gobe zaku haɗu a School, ko ka manta? Kuma sun ce zasu zo mana yawo mu ma." Murmushi ya saki haɗe da faɗin, "Yauwa Mami. Na ji daɗi da zasu zo gidanmu." Ya bi bayanta yana dariya. Har mota suka raka su sannan suka dawo gida. Fuskokinsu ɗauke da dariya. *** Tsaki ya yi a bayyane haɗe da ɗaukar wayarsa da ke ringing, ya kara a kunnensa da faɗin, "Hello guy." "Abokina ya dai?" Bobby ya faɗa da fara'a. "Ba lafiya fa guy. Akwai damuwa sosai. Ina tunanin ɓalli na neman kwancewa fa. Tun ɗazu nake kiranka baka ɗauka ba." Dafe kansa ya yi Bobby, ya tausasa muryarsa ya ce, "Tell me something, what is going on? (Ka faɗa min wani abu, me yake faruwa ne?" "Guy kiran da Dady yake min sanda nake gidanku ɗin nan, ashe laifin da na yi a company aka faɗa masa. Guy baka ga faɗan da ya min ba, ban taɓa tsammani ba. Kuma abun haushi hasarar da ta fi wannan ma na jawo amma bai min faɗa ba sai wannan. Kamar dai sai mun koma wurin boka, dan da alama maganarsa ke neman tabbata. Gwara tun wuri ai wa tufƙar hanci." Bobby ya ce, "Lallai kuwa. Daddyn ne ya maka faɗa? Akwai damuwa tabbas. Dole zamu koma masa. Gashi kuma yanzu dare ya yi. Sai dai gobe da sassafe na zo na ɗauke ka sai mu tafi." "To zan jira ka guy. Dan Allah kar ka bari na yita jiranka. Ka san a matse nake, kar a samu matsala mai girma." "Babu wannan a tsakaninmu, ka sani. Kawai ka jira ni da sassafe. Kar kuma ka sha komai, kar bacci ya ɗauke ka. Sai ka yi shigar zuwa wurin aiki, daga can kawai ka wuce aiki." Daga haka suka yi sallama zukatansu a raunane. Ummu Ayeesher where are you? Ban manta da ke ba. Gaisuwar taki ta musamman ce. Ina yinki irin sosai da sosai din nan. Duk members na NAGARTA WRITERS FANS na gaishe ku. Ina yinku irin totally din nan. Fatan kun san da hakan. Alhamdulillah! Jiki kam ya yi sauki sosai. Na gode kwarai da adduoinku. Allahu ya bar zumunci da zaman tare. What do you expect here? Shin wacece Dr. Islam din nan Maman Abdul? Menene dalilin kulla wannan alakar da marubuciyar ta yi? Modu mai matsalar zuciya, yaya abun zai kaya? Me Fiddou zata fada wa likita bayan kuma ita kanta bata san asalinsa ba? A dai juri zuwa rafi, wata rana tulu zai fashe. Marubuciyar zata yi amfani da alkalaminta wurin fayyace mana komai, kawai mu ci gaba da bibiyar labarin. Zamu yi mamakin komai a karshe. Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:47 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 32 Tun da sassafe ya hau shiri. Manyan kaya ya saka, farar shadda mai matuƙar kyau, an mata surfani da kalar baƙi. Hakan ya sa ya saka baƙar hula, baƙar agogo da kuma baƙin takalmi. Kallo ɗaya ka ma Annur zaka ji ya shiga ranka, kamar ba shi ne wannan mugun mashayin ba. Turaren cinema ya shafa a jikinsa sannan ya fesa explore. Lakar madobinsa ya jawo ya fiddo kuɗi ya saka a aljihunsa, sannan ya kama hanyar fitowa daga ɗakin nasa. Sai da ya fara biyawa part ɗin su Momy. Ya same ta a falo tana zirga zirgar haɗa kalaci ita da mai aikinta. Har ƙasa ya duƙa ya gaishe ta. Akwai fa ladabi ko ba komai. Ko da yake, dama an ce wai masu irin mugayen halayen nan sun fi kowa ladabi da girmama na gaba da su. Ladabin kunama ke nan. "Ya da fitowa haka tun da wuri?" Ta faɗa bayan ta iso daidai inda yake zaune. "Yau da wuri nake son zuwa aikin ne Momy. Akwai ayyuka da dama da nake son na warware su." Ajiyar zuciya ta sauke tana binsa da kallo. Kallon yanayin nasa na yau. Babban mutum mai ƙwarjini a fuska, sai dai kuma babu halaye na gari. Ya yi rashin halayen kirki tun shekaru uku da suka gabata. Ko ma fin hakan. "Annur dan Allah ka kula. Ka ga ka ɓata wa mahaifinka rai ba kaɗan ba. A kiyaye gaba, bana fatan hakan ta sake faruwa nan gaba. Ka ji?" Miƙewa ya yi ya zauna bisa kujera, yana sosa ƙeyarsa ya ce, "Insha Allahu Momy na miki alƙawari hakan ba zata sake faruwa ba." "Ina fatan hakan, Annur. Allah Ya maka albarka ya ƙara shirya ka, ko ka samu ka ajje hankalinka wuri ɗaya ka tsayar da matar aure." Bai furta komai ba wayarsa ta ɗauki ƙara. Dubawar da ya yi ya ga Bobby ne ke kiransa ya sa shi saurin miƙewa a kan kafafuwansa. Ya ce, "Momy har an fara kirana. Usman ne secretary na san jirana yake. Zan tafi, sai na dawo." "Au! Kalacin ma ba zaka tsaya a kammala ba?" Taku ya yi haɗe da furta, "Ina sauri ne Momy. Ina son gyara kuskuren da na tafka a baya. In gyara tsakanina da Dady." Da fara'a ta ce, "Allah Ya tabbatar da hakan. Ina ji a jikina dai hakan ya zama alkhairi. Dan ga zahirin canji nan na gani a tattare da kai. Kai ɗin nan da baka tashi tafiya aiki sai ƙarfe goma, amma gashi yau ko bakwai bata cika ba zaka tafi. Na ji daɗi ƙwarai." "Na wuce, Momy." A ransa mummanan ƙuduri ne kawai, a daidai ƙofar ya gyaɗa kansa haɗe da sakin murmushin ƙeta, wanda ya bayyana zallar muguwar manufarsa a daidai lokacin. Daidai zai shiga mota ya latsa kiran Bobby. Kamar yana jiransa kuwa ya ɗauka yana faɗin, "Am on my way." Kawai ya latse kiran ya shiga motarsa ya kunna. Kai tsaye gidan su Bobby ya nufa. Ya same sa a tsaye bakin gate yana jiransa. Shiga gaban motar kawai ya yi suka kama hanyar Jani sai wurin boka Gagarabadau. Yanda suka saba yi idan sun je wurin bokan suka yi. Bayan sun sha jini boka ya shanye sauran, sannan ya fuskanci Annur da faɗin, "Akwai matsala ne a aikin. An samu an fitar da ƙaunar da kake ma ɗaya daga cikinsu. Amma ɗayar na kasa ganin komai game da ita. Aikin da na yi a kanta a gabanku ya yi, amma washe gari na kasa fahimtar abin da ke faruwa. Wani irin haske ya ringa mamaye ƙwaryata a duk sanda na tura masu aljannu. Har na gaji na haƙura. Dan haka wannan aikin naka ne. Ni ba zan iya ba, kar wani abu ya faru kamar yanda ban taɓa tsammani ba. Yau ni Gagarabadau an samu abin da ya gagare ni. Ban san dalili ba. Ka ƙoƙarta fitar da ita daga zuciyarka, idan ba haka ba kuwa asiri na daf da tonuwa." Cike da tsoro da fargaba Annur ya ce, "Boka a dai ƙara ƙoƙartawa. Ban san ya zan yi ba idan wannan mugun ƙullin ya kwance. Ban kuma san yanda zan yi na fitar da yarinyar daga zuciyata ba. Ni kaina jinta nake a raina, duk yanda zan yi na fidda ƙaunarta na kasa. Har ƙudira na yi zan hukunta su amma na kasa. Na rasa me zan yi boka Gagarabadau!" "Aljannu basa magana biyu. Ka tashi ka tafi ka bani wuri! Kar kuma ka sake dawo min har sai ka fidda wannan soyayyar daga ranka. Idan ka jinkirta kuma, ka shirya zama abun tausayi, dan komai sai ya lalace." Kansa ya dafe Bobby, yana tsananin jin tausayin abokinsa. Ya rasa ta inda ma zai fara. Da ƙyar ya samu ya ce, "Boka a dai taimaka mana. Ka san gare ka kaɗai muka dogara. Kai ne kake rufa mana asiri, a yanzu ma muna neman rufin asirin nan. A duba wannan zancen boka, a bamu mafita." Manyan zane ya ringa yi a hannunsa na hagu, cikin wata irin murya ya ce, "Duba ku gani!" Ya juyo masu da hannunsa da ke fitar da haske. "Babu nasara ko kaɗan. Akwai abin da wannan yarinyar ta taka wanda tsafi ya gagara yi mata wani abu. Idan da hali dole sai ta shagala da aikin ta ajje sa, ko zamu samu nasara a kanta." Shiru suka yi su duka suna tunanin mafita. Ko kaɗan basu da idea a kan abin da zasu yi, kawai dai basu so bokan ya gajiya da su ne. "Zamu ƙoƙarta boka. Zamu san yanda zamu yi dan ganin yarinyar ta shagala da aikin nata. Muna godiya da ƙoƙarinka." kuɗi Annur ya ajje masa sannan suka miƙe a ƙafafunsu. Tunani fal a zukatan ko wannensu suka bar gidan. *** Zama ta yi a bisa kujerar da ke fuskantar tasa. Idanuwanta a raunane take kallonsa. Zuciyarta fal da tunanin abin da zata faɗa ma likitan. Muryarsa ce ta dakatar da ita daga tunanin da take, ta dawo da hankalinta gare shi, tana sauraren abin da yake faɗi. "Giɗe ki kwantar da hankalinki hwa. Abin da na hwaɗi ba lallai bane ya tabbata, hasashe ne dai kawai nai yi. Yanzu dai ki hwaɗi min. Halan mi as silar haukan can nashi? Ta haka kawai zan tabbatar da hasashen da nake yi a kan giɗe." Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke. Cikin wata murya rinanna ta fara bashi labari. * Tafiya yake da ƙafafuwansa, kayan jikinsa sun yayyage, tsiraicinsa duk ya bayyana, yana kuka kamar ransa zai fita. Gajiya ya yi sosai da tafiyar, jiri na ɗibarsa sosai, hakan ya sa ya fara dafe kansa, da ƙyar ya samu ya duƙe ƙasa, yana wani irin kuka mai tsuma zuciyar duk wanda zai ji sa. Tun sanda yake tafiya take kula da shi, take bibiyar lamurransa, har sanda ya gaji da tafiyar ya tsaya a ƙafafuwansa. Ya kuma gaji da tsayuwar ya tsuguna a guiwowinsa. Cike da tausayi ta ƙarisa inda yake, tana jin tsanan fargabar tinkararsa. Sai dai kuma duk da hakan, bata jin ko kaɗan zata iya tafiya ta bar shi a wannan halin ba. Ko kaɗan ba zata iya fitar da tunaninsa daga cikin zuciyarta ba. "Giɗe." Ta faɗa cikin sanyin murya. Zuciyarta na dukan uku-uku, ba ma ta san ta inda zata fara ba. Ɗagowa ya yi da rinannun idanuwansa ya dube ta. Duba ta tsanaki kafin ya sake duƙar da kan nasa, yana mai ci gaba da kukansa. Dakewa ta yi ta sake furta, "Giɗe ba zan cutar da kai ba, Allah kuwa da gaske nake." Bai ɗago kanshi ba a wannan lokacin, sai ƙara ɗaga sautin kukan nasa da ya yi. Duƙawa ta yi a gabansa, tana jin duk wata fargaba na fita daga zuciyarta. Zallar son taimaka masa ne a cikin farar zuciyarta. "Giɗe ka hwaɗi min do Allah de. Mi ka damunka?" Sai sannan ya ɗago fuskarsa yana gwada mata cikinsa da hannuwansa. Alamun yunwa yake ji sosai, da alama ita ce ta galabaitar da shi. Bata fahimci manufarsa ba, sai faɗin ta yi, "Cikinka yake maka ciwo? Bara na kawo maka magani yanzu. Dan Allah kar ka tafi, ka ji?" Kansa ya gyaɗa mata, yana sake nuna mata cikin nasa da duka hannuwansa a wannan karon, ruwan hawaye na sake wanke masa fuska. "Mina ne halan giɗe? Ko yunwa kake ji?" Saurin ɗaga mata kai ya yi, kukan da yake lokaci ɗaya yana sauyawa zuwa murmushi, murmushin da duk ƙazantar fuskarsa bata hana kyawunsa bayyana ba. Murmushin ta yi ita ma, duk da tausayinsa da take ji, da damuwar da ke cikin zuciyarta. "Zauna a nan kar ka tafi. Yanzun nan zan kawo maka abinci." Bai ce da ita komai ba sai murmushinsa da ya faɗaɗa, ya gyara zamansa yana bin bayanta da kallo. Ta ɗan jima bata dawo ba sai gata ta taho da plate ɗin abinci a hannunta an rufe, sai kuma wani yaro biye da ita, wanda zai tafi da plate ɗin idan an gama. Yana ganinta ya hau murmushi, da haƙoransa a yaƙe, yana miƙo mata hannu tun bata ƙarisa isowa inda yake ba. Zama ta yi a kusa da shi, ta motsa shinkafa da miyar da cokali, sannan ta miƙa masa tana murmushi ta ce, "Ka ci gashi. Ga kuma ruwa nan idan zaka sha." Bai bi ta kan karɓar ruwan ba. Cokalin ma yar da shi ya yi ya ringa cin abincin hannu baka hannu ƙwarya. Kyakkyawar loma biyar ya cinye baki ɗaya abincin, ya miƙo mata hannu ta bashi ruwa. Tsabar sauri ya sa ya gagara fasa ledar ruwan ma, ya ringa kai shi bisa leɓonsa ya kasa buɗewa. Karɓa ta yi ta fasa masa, sannan ta miƙa masa a daidai bakinsa. Zuƙa ɗaya ya shanye duka ruwan ledar, ya saki kyakkyawar gyatsa, alamun ya ci ya ƙoshi ke nan. Miƙa wa yaron plate ɗin ta yi, ta ce, "Giɗe tahi ka kai mata, na gode ma ka jiya." Ya karɓa ya tafi, yana yi yana ɗan waigen mahaukacin, wanda al'aurarsa take bayyane. Ganin irin kallon da yaron yake binsa da shi ya sa ta yi saurin cire ɗan ƙaramin mayafinta, ta lulluɓe masa jikin nasa, tana mai tsananin tausaya masa. Rasa yanda zata yi da shi ta yi, miƙewa ta yi bisa ƙafafuwanta, tana faɗin, "Giɗe tashi mu tai gidanmu. Ina baka ƙarin wani abinci ka ci." "Zaki kai ni wurin Amrah?" A ba zata ta ji maganar tasa, dan bata yi tsammanin ko magana ya iya ba. Ta dai tabbatar ba kurma ba ne, saboda yana jinta, kuma yana yin duk abin da ta ce masa ya yi. Da murmushin yaƙe ta ce, "Zan kai ka mana. Amrah ko?" Dariya sosai a fuskarsa ya ce, "Ehh, Amrah fa. Wallahi ita nake so, AMRAH NAKE SO!" "To can zan kai ka. Mu tahi." Ta tasa shi gaba tana binsa a baya. Duk ta inda suka gitta binsu ake da kallo, kallon tuhumar inda ta samo wannan ƙazamin matashin, sauƙinta ma yanda ta ɗaure masa ƙugunsa da mayafinta, ya rufe tsiraicinsa da ya bayyana. Kallon da ake mata ko kaɗan bai sa ta ji ko ɗar a jikinta ba. Sai ma ƙoƙarin jansa fira da take, amma ko kaɗan baya amsa ta. Shiru ya yi, kuma bata yi shirun ba ita. A daidai ƙofar gidansu suka isa. Gabanta ya tsananta faɗuwa a lokacin, tana tsoron yanda zata shiga gidansu da shi, haka kuma bata jin zata iya barinsa haka ya tafi, ba tare da ta samar masa suturar kirki ya suturce jikinsa ba. Kuma ta tabbatar cewa bai ƙoshi da abincin da ya ci ba, saboda halam halam ɗin da ta ganshi yana yi. Runtse idonta ta yi tana tunanin mafita. Tana buɗe su ta dire bisa fuskar Yayanta, yayanta da take shakku, take matuƙar jin tsoronsa. "Yaya...uhm..." Ta samu ta matso da ƙyar, tana jin wani sauyi a duniyarta, ƙirjinta sai tsananta duka yake. "Foddousi mi halan? Ina kika samo giɗe gashi nan tsaye?" Kyarmar laɓɓa ta fara yi. Da ƙyar ta samu tattara laɓɓanta wuri guda, ta tsaida tunaninta wuri ɗaya, hankalinta duka ya koma ga yayan nata. Ta sanshi, ta san halinshi. Ko kaɗan baya son wasa, baya son yana magana ana ƙyale shi. Hakan ya sa ta fara magana da rawar murya, "Yaya a saman godabe na haɗu da shi, cikin halin tashin hankali, ga tuhwahi nai a yage, jiki nai ya bayyana, dan shi ne nat taho da shi. Ina tausai nai ne." Wani irin wawan kallo yayan nata ya bi ta da shi. Take Fiddou ta raina kanta, jikinta ya fara rawa tana tunanin mafita. Bata samo mafitar ba ta ji muryarshi yana faɗin, "Kina ɓace min ko sai na ɓaɓɓalla ki? In banda hauka da shashanci, daga haɗuwa da mahaukaci bisa godabe sai taimako? Ke ko san mutanen yanzun ga yanda suke abin tsoro? Haka ɗai muna zaman zamanmu ki jawo mana bala'i inda muke, sam! Ban lamunci wanga hauka ba. Kuma ki tahi daga wurin ga tun ban saɓa miki ba." Sosai jikinta ya tsananta kyarma. Tana tsananin tsoronsa, amma duk da hakan bata jin zata iya tafiya ta bar shi a wurin ba tare da ta san inda zai nufa ba. Suna cikin haka wayar yayan nata ta hau ƙara. Ɗauka ya yi suka gaisa da mai kiran nasa, sannan ya shaida masa cewa ya gaggauta dawowa kasuwa, an samu mai siyan dozen biyu na takalma. Da murnarsa ya tsinke wayar. Yana jin daɗin cikin da zai yi a lokaci guda. "Giɗe ki hankali. Zan tahi yanzu, amma walle ki tabbatar ke shiga gida, tahi ma tun yanzu ina kallonki." Ta ɗan samu sassauci a zuciyarta. Daurewa ta yi ta shiga gidan, ya tabbatar ta shiga sannan ya karya kwana, yana mai son dakatawa ya kori mahaukacin daga wurin, amma kuma yana ji kamar idan ya tsaya zai iya rasa cikin da tun ɗazu yake so ya yi, amma kuma babu kasuwa. A zaure ta tsaya tana leƙensa har sai da ta tabbatar ya ɓule, sannan ta fito tana masa murmushi. This page is in your honour, Asea Bashir Aliyu (Asisi). Ina yinki irin sosai da sosai ɗin nan. Ina ƙaunarki fi sabilillah. Kin sani kuwa? Ko ta wace hanya su Annur suke ga kaman zasu shagaltar da rayuwar Maryama? Shin zasu yi nasara kuwa? Miye dalilin da ya sa asirin ya gagara tasiri gare ta? Me kuka hasko a cikin wannan labarin da Fiddou ke ba ma likita? Na gode ƙwarai masoyana. Ina son ku all fi sabilillah. Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:48 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 3⃣3⃣ Bakin wani tsohon gini ta nufa da shi, ginin da alama babu mutane a cikinsa. Da murmushi a fuskarta ta ce, "Bara na kawo maka tabarma, ina zuwa." Bai ce da ita komai ba, a tsaye yake yana binta da kallo, har sanda ta je gidansu ta dawo. Wata tsohuwar tabarma ce duk ta gama yaƙunewa ta shimfiɗa masa. Bayan ta daidaita ta ta ce, "Taho zauna ka huta giɗe. Dan da ganinka ka gaji ko tantama babu. Ka ga hwa yanda ƙahwarka ta tsatssage." Bai musa mata ba ya zauna a bisa tabarma, ya dunƙule baki ɗaya jikinsa, sai faman kyarma yake. Ganin kyarmar da yake ta tsananta ya sa hankalinta tashi, ta ce, "Giɗe mi ya hwaru kuma?" Bata tsaya jin komai daga gare shi ba ta kara hannunta a wuyansa. Zafi ta ji rau kamar garwashi. Ta kuma dafe masa kai, nan ma zafi ta ji sosai da sosai. "Giɗe baka da lahiya walle. Yanzu ya zan yi da kai?" Hawaye ne ta ji suna zarya a kumatunta. Shi kanshi mahaukacin ruwan hawaye ne ke kwarara a kumatunsa, wanda na azabar zazzaɓi ne kawai. "Bari in ga ko ina samo ma magani." Ta tashi da hanzari ta nufi gida. A ɗakinta ta ci burki, ta hau bincikar lakokin madubinta a haukace, tamkar ciwon a jikinta yake. Da ƙyar ta samu ta gano katin paracetamol, wanda guda biyu tal ya rage a jiki. Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta miƙe, ta fito daga ɗakin nata, ta nufi kitchen. Kofin roba ta ɗauko ta nufi randar ɗibar ruwa, ta ɗiba zata bar wurin ke nan ta ji muryar matar yayanta cikin masifa ta ce, "Ke Fiddou halan ina zaki tai min da kohi?" Jikinta na rawa ta rasa me zata faɗa, tana gudun tonuwar asirinta. Saboda sam matar yayan nata bata da kirki, abu kaɗan zata mata ta kai ta ƙara a wurin yayanta, shi kuma babu bincike kawai ya hau hukunta ta. "Fiddou halan kin zama kurma ne?" Ta sake jiyo muryar matar cikin ƙaraji. "Giɗe ajje min kohi, dan na ga alamun baki da gaskiya ne." Bata da wani zaɓin da ya wuce ta juye ruwan, sannan ta koma kitchen ta ajje ranta a ɓace. Tana ƙara tuna cikin halin da ta baro mahaukacin. A saɓule ta fice daga gidan, tana jiyo muryar matar yayan tana ƙwala mata kira amma ta mata banza, dan bata jin zata iya ƙyale mahaukacin a cikin yanayin da ta baro shi. Wani shago ne kusa da su ta nufa. A can ta roƙi mai shagon shi ya bata ruwan leda guda ɗaya, idan ta koma gida zata kawo masa. Bai ko musa mata ba ya ce ta buɗe fridge ɗin ta ɗauka. Ɗaukar kuwa ta yi, sannan ta kama hanyar kangon da ta kwantar da shi. Karkarwar da ta samu yana yi ta fi waccen ta farkon, abun nashi ya ta'azzara sosai. Hankalinta ya matuƙar tashi, gabanta ya tsananta duka, tana masa magana amma tamkar ma ba da shi take ba. "Giɗe yi haƙuri do Allah de, ka daure ka tashi ga magani nan na samo ma. Insha Allahu da ka sha kana samun sassauci." Buɗe idonsa ya yi ya sauke a kanta. Yana son ya tashi amma ya kasa,nauyi yake jin jikinsa na masa ƙwarai da ainun. Cikin tausayi ta kama shi ta tasar zaune, ta jinginar jikin bangon wurin, tana son ganin ya buɗe idonsa dangar-gar a fuskarta amma ya kasa, duk yanda ya buɗe su dole sai ya rufe, saboda zafin zazzaɓi. Ɓallo masa maganin ta yi sannan ta miƙa masa, bai jira wata wata ba ya jefa bakinsa. Tana ƙoƙarin fasa ruwan ta bashi amma har ya taune maganin, shi ko ma ɗaci bai ji ba. Sai da ya taune tas sannan ta ce masa, "Inhi ga ruwa giɗe. Sha ko maganin na saurin yi maka aiki." Karɓa ya yi ya kai bakinsa. A raunane take binsa da kallo. Tana tausayinsa sosai, tana mai tsananin jin shi a cikin zuciyarta. Bayan kamar kwana uku mahaukacin ya ji sauƙi sosai daga zazzaɓin da yake. Saboda Fiddou ta kira wani malamin asibiti har cikin kangon da yake ya duba sa, ya tabbatar cewa wahala ce kawai, saboda yanayin nasa, da kuma yanda ƙafafuwansa suka koma, da alama ya yi tafiyar ƙasa mai matuƙar yawa, wadda ita ce ta galabaitar da shi, har ya tsinci kansa a wannan yanayin. Tun bayan da ya ji sauƙi ta saka masa suna Modu, saboda sunan mahaifinta da ya rasu Muhammadou, tana matuƙar son mahaifin nata, shi ya sa ta masa takwara da mutumin da ta kamu da tsantsar ƙaunarsa cikin lokaci kaɗan. A wannan kangon da yake ne wata rana aka ce za a ci gaba da ginin, saboda masu gidan suna so su dawo. Hakan ya sa ta mayar da shi can tsallaken titi, shago ne wanda babu kowa a cikinsa, jikin gidan su wata ƙawarta suka ce mata ya zauna, har sanda zasu nemi shagon. Yayanta kuma ya gaji ya ƙyale ta, ganin bashi da yanda zai yi da ita, ta riga da ta sa ma ranta ƙaunar Modu. Abinci ma ya amince mata tana kai ma Modu, sai dai matarsa ce marar kirkin, ba dai da izininta a kai abincin ba, sai idan Yayanta yana nan. Idan baya nan kuwa dole sai dai ita Fiddou ɗin ta ɗauki nata ta kai wa Modu. *** "A ranar da wannan haɗarin ya hwaru, na jima ban kai masa abinci ba ne, hakan ya sa ya nemi ƙetare godabe da kai nai, zai tai inda nike. Kaji abin da ya hwaru likita. Ni kaina ban san Modu ba, ban san asali nai ba. Da hauka nai na ganshi. Sai dai abin da na sani game da shi kawai, yana yawaita kiran sunan wata, yana yawan yin kuka a lokuta da dama idan ya tuna ta." Tana kai wa nan ta kalle shi, tana kallon yanda yanayin likitan ya sauya, kamar ba shi ba. "Halan mina ne sunan wadda yake kira ɗin ma? Sister ta hwaɗi min kuma na manta sunan." "Sunanta Amrah. Ina jin a jikina wata ƙila mata tai ce. Dan in ba mata tai ta ba, ban ga dalilin da zai na hwaɗin sunanta ko yaushe ba." Rubuta sunan ya yi a takarda, kafin ya ce, "Yanzu dai tun da ya ji sauƙin wanga haɗari da ya hwaru, ina ganin kawai zan yi maku reffer daga wannan asibiti zuwa asibitin gwamnati. A can ne ad da ma'aikata ƙwarai da kuma kayan aiki masu tsada. Akwai abokina likitan zuciya, zan haɗa ku da shi, na san zai kula da giɗe ƙwarai, kamar yanda zan kula da shi." Godiya ta masa sosai kafin ta miƙe a kan ƙafafuwanta, ta share guntuwar ƙwallarta, ta ce, "Bari in tai likita, ina jiranka cikin ɗaki nai." Kai kawai ya ɗaga mata, kafin ya ci gaba da rubutunsa, ita kuma ta kama hanyar fita. *** A hanzarce ta lalubo wayarta da ke ruri a cikin jaka, tana gudun kar ta tsinke, saboda jimawar da ta yi tana ringing ɗin, sannan kuma wannan shi ne kira na huɗu da aka mata, tana cikin napep bata ɗaga ba. A hankali ta murmusa ganin sunan wanda ya kira ta ɗin, ta kara a kunnenta da faɗin, "Wa ke magana?" Cikin mamaki ya zaro ido kamar tana gabansa ne. Ya ce, "Jiddah, ba dai baki da lambata ba." "Mallam ka kira kana wani faɗin ba dai bani da lambarka ba, kai ɗin waye da za a ce dole sai na yi lambarka a cikin wayata?" Cikin sanyin murya Annur ya ce, "Calm down, Annur ne." Tana jin yanayin da ya yi maganar ta tabbatar akwai damuwa, akwai abin da yake so ne kamar yanda take buri. "Ehen, go on." Ta faɗa cikin muryar faɗa. "Please Jiddah...please ki taimaka min. Dan Allah lambar ƙawarkin nan Maryama nake so ki turo min." Janye wayar ta yi daga kunnenta tana bayyanannen murmushi, a ranta tana faɗin 'Tarkona ya kama kurciya.' Samu ta yi ta mayar da wayar a kunnenta, ta ce, "A kan me zan baka lambar Maryama? Me zaka mata?" Cike da damuwa ya ce, "Ina ƙaunarta ne, kamar yanda na faɗa miki a baya. Wallahi bana nufinta da komai face da alkhairi. Ba zan taɓa cutar da ita ba." Ajiyar zuciya ta sauke ta ce, "Zan turo maka lambar Maryama, amma fa sharaɗi guda, duk abin da ya faru da ita kai ne. Ka amince?" Da sauri ya ce, "Ehh, ehh wallahi na amince, na amince Jiddah." "To, zan turo maka yanzu idan mun gama waya. Amma kar ka kira ta sai dare, saboda yanzu ban riga da na faɗa mata ba." "Ok, thanks." Ya furta cike da farin ciki. Tana kashe wayar ta kashe recording ɗin da ta yi, ta yi savinginsa a kan wayarta sannan ta lalubo lambar wayar Maryama ta kira ta. "Hello Jiddah." Maryama ta faɗa cikin sassanyar muryarta. "Maryama hau watsapp yanzu zan turo miki wani audio." "Ok." Kawai ta faɗa haɗe da tsinke wayar ta buɗe datarta. Tana saurare tana murmusawa. Sosai hakan ya mata daɗi, dan su a tunaninsu ko haƙarsu ce zata cimma ruwa. Basu san cewa wani mummunan ƙudiri ne a zuciyar Annur ba. Duk da yana son Maryama, yana ƙaunarta har cikin zuciyarsa, baya jin ko kaɗan zai juri fallasar asirinsa. Zai haƙura da ita, ko da hakan yana nufin ƙarshen numfashinsa, matuƙar dai asirinsa bai tonu ba. Voice note ta ma Jidda cewa lallai sun yi sa'a sosai, su da suka ji shiru sun ma zata ko komai nasu ya lalace. A ƙarshe dai haka Maryama ta ƙarisa yinin ranar zuciyarta fal da farin ciki, tana jiran dare ya yi ko zai kira ta, ta ji yanda zasu kaya. Ana yin magrib sai ga Bobby ya kira ta. Haushinsa ta ji dan ta yi tsammanin Annur ne. Bata tsayar da adhkar ɗin da take ba kawai ta latse silence, tana mai ci gaba da addu'o'inta. Jin Bobby ya sake kira ya sa kawai ta mayar da wayar silent baki ɗaya, sannan ta ci gaba da addu'arta. Bayan sallar isha'i ta miƙe, ninke hijabin ta yi ta ɗora bisa kafet, sannan ta nufi falo inda iyayenta suke. Sam! Ta manta da bata cire wayar daga silent ba. Annur kuwa kiran Bobby ya yi a waya cewa ya gama tsara komai, da yamma ya koma wurin boka ya sanar da shi duk ma yanda zai yi ya ƙoƙarta fara aikin a cikin daren nan, saboda zai san duk yanda zai yi ya shagaltar da ita, ya yaudare ta, har ta rasa yin ibadar da ta saba yi a cikin dare. Sosai Bobby ya ji daɗin hakan, yana son farin cikin abokinsa, yana son ya ga sun yi nasara a wannan aikin. Bayan ta je falo ta tarar Mama zaune, sai Abbanta da Muhammad da dawowarsu ke nan daga masallaci sun yi zaune a ƙasa, suna zaman jiranta. Cikin ladabi ta gaishe da Abbanta. Da fara'a tana mai gasgata masa irin kewarsa da ta yi, saboda cikin kwanakin nan bai cika samun zama gida ba sosai. "Kin yi zaune Maryama. Ki kawo mana abinci, na san wannan kasan bacci yake ji, dan gashi nan ya fara hamma." Miƙewa ta yi tana miƙa, ta ce, "Ai Mama ba wai Muhammad kaɗai ba, ni kaina yau baccin nan nake ji. Ina son na kwanta da wuri, saboda zan tashi ƙarfe sha biyu, karatu nake son yi sosai, gobe zazzafan rehearzal ne." "To fa! Maryam ashe abun ya matso dai. Yaushe ne zaku yi wai?" Da fara'a ta ce, "Ashirin da biyar ga wannan watan ne Abba. Yau saura kwana goma sha huɗu ke nan, tun da yau sha ɗaya ga wata." "To masha Allahu! Allah Ya nuna mana Maryama. Ina alfahari da ke." Murmusawa ta yi haɗe da barin falon, ta nufi kitchen domin kawo masu abinci. Tuwon alkama ne da miyar ɗanyar kuɓewa. Ci suka yi suka ƙoshi, a lokacin tara ta yi. Sun bari abincin ya bi jikinsu sannan Maryama ta tayar da Muhamnad tsaye, ta ce, "Oh ni Hammad! Kai gaka nan kaman ba namiji ba. Wai gyangyaɗi yake Mama, abun dariya." Dariya suka yi su duka ɗakin, kafin Maryama ta kai Muhammad ɗakinsa, ita ma ta wuce nata ɗakin. Hamdala ta yi ga Allah, ta fiddo Qur'aninta daga cikin jaka ta ɗora bisa kafet, yanda idan ta tashi da dare ba sai ta nema ba. Hayewa ta yi bisa gado tana miƙa da hamma duka a tare, sam! Ta manta da wayar da Annur zai kira ta, gashi kuma ta saka wayar silent. Har ta kwanta kuma ta tuna da bata yi alwalar kwanciya barci ba, hakan ya sa ta miƙe da bacci sosai a idanuwanta. Sosai shaiɗan ke riya mata yau dai ɗaya ta haƙura da alwalar nan, saboda baccin da take ji. Ƙoƙari ta yi ta kawar da shaiɗanin, ta miƙe ta yo alwalar, sannan ta kwanta. Sai da ta tofa addu'a sosai bacci ya yi awon gaba da ita, ga ƴar agogon da ke tada ta daga bacci a gefenta. To me kuka ce masu karatu? Boka Gagarabadau zai iya aiki ga Maryama kuwa? Ya kuke ganin larurar Modu? Ko zai haye daga wannan mummunan ciwon zuciyar da ya kama shi? Zaku samu duka amsoshin nan daga bakin Amrah. Mu dai namu kallo ne kawai, sannan mu mata voting idan mun gama karantawa. Masu karatu sai kun yi haƙuri yanzu kam, saboda ba kullum zaku ringa ji na ba. Na dawo gida ne, kuma dole akwai abubuwan da zasu ringa shan kaina. Sai dai zan maku alƙawarin ƙoƙartawa bakin gwargwado, har sanda zamu kai ƙarshen labarin. Sai dai fa ku sani, akwai sauran labari sosai nan gaba. Allah Ya nuna mana mun kai aya. Ameen. Thanks all. Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:49 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 3⃣4⃣ Wannan ne karo kusan na goma sha biyu da Annur ke kiran Maryama amma ta ƙi ɗauka. A ƙarshe ya latsa kiran Jiddah zuciyarsa raunane, yana fatan ita ɗin ta ɗauka, ko zata kira masa Maryama a kan ta daure ta ɗauki kiransa. Ringing ɗaya wayar Jiddah ta yi ta jawo ta daga jikin caji, sunan mai kiran da ta gani ne ya sa ta hanzarta ɗauka da sallama a bakinta. Bai ko amsa ba ya ce, "Please Jiddah ko baki faɗa wa Maryama cewa zan kira ta ba? Ina ta kiranta ta ƙi ɗauka, kuma gashi dare bai wani yi ba bare a ce ko ta yi barci ne." Cikin mamaki Jiddah ta ce, "Na faɗa mata mana. Amma kashe zan kira ta in sanar da ita, wata ƙila bata gane lambar taka ba ne." "Ok please ina jiranki Jiddah." Annur ya faɗa haɗe da kashe wayar. Yana kashewa ta latsa kiran Maryama, sai dai da mamakinta ta ƙi ɗauka. Sai da ta kira ta sau biyar amma shiru. Cikin takaici ta ce, "Why Maryama, why? Me ya sa zaki nemi tarwatsa mana plan? This is what we've been waiting for, gashi damar ta zo kuma kina neman ɓarar mana da ita." Tana faɗin haka tana sake kiranta, amma shiru bata ɗauka ba. "Oh God! Maryama kin kofsa mana da kika yi baccin nan da wuri. Allah dai Ya sa kar shirinmu ya ɓaci." Ta latso kiran Annur. Yana ɗauka ta ce, "Ina ta kiranta bata ɗauka ba, da alama dai ta yi bacci. Dama fa Maryama akwaita da kwanciya da wuri. To da alama dai sai dai ka kira ta wani lokacin." Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke Annur, ba tare da ya sani ba ya ce, "Maryama why do you want to ruin our plan? Please pick up my call..." Bai gama maganar ba ya yi saurin dafe bakinsa, yana tunanin yanda maganar ta suɓuce masa ba tare da ya san ya yi ba. 'Me ya sa take son lalata masu plan?' Jiddah ta tambayi kanta, take gabanta ya hau dukan uku uku, kar dai a ce fa Annur sun gano su ne, wata ƙila suke neman ɗana masu wani tarkon. "Wane plan kake magana? What do you mean?" Ya jiyo muryar Jiddah ta tambaye sa, muryar kaɗai ka ji zaka tabbatar da cikin tashin hankalin da take. "Ahm...uhm dama...uhm, I just, I just need her by my side. I love Maryama with all my heart. I want her to be my partner, abokiyar rayuwata ta har abada." Duk da faɗin hakan da ya yi bai sa gaban Jiddah ya daina faɗuwa ba. Ta san Annur, ta san waye shi. Ta san cewa zai iya aikata komai domin farin cikinsa, haka Bobby ma. Tana gudun su cutar da Maryama. Sai yanzu take tunani lallai sun tafka babban kuskuren fara wannan plan ɗin. A ganinta shi ke nan komai ya lalace. "Uhm, Jiddah kina ji na? Please ko lambar Maman Maryama zaki taimaka ki turo min? I mean her mother's phone number. I really want to talk to Maryama." "Are you out of your sense? A kan mene zan baka lambar mahaifiyarta? Idan ma ka sha wata banzar ƙwayarka ne da take faɗa maka wannan banza banzar to ka gaggauta neman gishiri ka sha ko zata fice. Dan wannan gurgun tunani ne kake, wanda ba zai taɓa yiuwa ba." Sosai muryar Annur ke rawa, ya ce, "Please help me Jiddah! Ba zan iya bacci ba tare da na ji muryan Maryama ba. And..." Ya dakata daga nan, yana ƙoƙain haɗiye damuwarsa, tunanin yanda suka yi da bokansa ne ya faɗo masa a rai. * "Kana min wasa da hankali sosai Annur. Abu ya ƙi ci ya ƙi cinyewa. Shin ya muka yi da ku ɗazu?" Cike da rauni ya kalli bokan, yana son yin magana amma tsoron furta komai yake. "Kamar yanda na faɗa maku ɗazu, ku tabbatar kun shagaltar da ita matuƙar kuna so aiki ya yi tasiri a kanta." Sai a sannan ya iya ɗaga laɓɓansa, cike da rauni ya ce, "Boka Gagarabadau, abin da nake son aikatawa ke nan. Sai dai kuma ina buƙatar taimakonka. Dole sai ka saka hannu a wannan lamarin ko zai iya kasantuwa." "Babu wannan maganar Annur. Ka tashi ka tafi kawai, bani da abin da zan iya yi maka." Har ya miƙe kuma ya dawo ya zauna. Ya fuskanci bokan da jajayen idanuwansa da suke neman kawo ruwa, ya ce "Zan yi Ya bokana! Na maka alƙawarin duk yanda zan yi yau sai na yi domin gyaruwar wannan aikin. Yau nake son aikata komai, kai ma ka shirya yin aiki a kanta a cikin daren yau. Ina baka tabbacin komai zai koma daidai, zan fitar da ƙaunarta daga zuciyata, a ƙarshe a samu gyara min wancan aikin na farko." Murmusawa baƙin tsohon ya yi sosai, har sai da haƙoransa da suke cike da baƙin gashi suka bayyana. Ya ce, "Bana jin ka Annur. Na tabbata zaka yi. Zan kashe duk wani aiki nawa na dare, zan tare ga aikin wannan yarinyar, a cikin daren nan za a gama komai." Cike da yaƙini Annur ya zaro kuɗi daga aljihunsa ya dire a gaban boka. Jinjina masa kai bokan ya yi, kuɗin suka ɓace daga gabanshi, sannan ya ma Annur umurni da ya tashi ya tafi. * "Na roƙe ki Jiddah, ki taimaka min. Na miki alƙawari ba zan cutar da ita ba." Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke jiddah, tunani take shin ta bashi lambar Mama ko kuwa dai kar ta bashi? Babbar matsalar ita ce kar Mama ta gano halin da suke ciki, ta san komai zai iya faruwa, tun da ba gaskiya Maryama ta faɗa mata ba. "Ka yi haƙuri Ya Noor. Na tabbata gobe idan Maryama ta ga missed calls ɗinka zata kira ka." Kashe wayar ya yi ba tare da ya sake furta komai ba, yana jin yanda zuciyarsa ke tafarfasa, take hararo masa bokansa da yake can sake da baki zai masa aiki yau. Latsa kiran Bobby ya yi, cikin rauni ya ce, "Guy akwai damuwa..." Ya kwashe komai ya sanar masa, ya ƙara da faɗin, "What are we going to do now?" Shi kanshi Bobby ɗin damuwa ce fal a zuciyarsa. Ya ma rasa ta inda zasu ɓullowa lamarin, ya sani, ya san sarai boka Gagarabadau baya son wasa, ko kaɗan baya so ana kawo wargi a harkarsa. "Ka yi shiru Farouk. Please ka faɗa min, ya zan yi?" "Calm down abokina. Be a man, ban sanka da rauni irin wannan ba. Yanzu abin da zai faru, kawai ka haƙura da wannan batun na yau. Gobe da sassafe sai ka zo mu tafi wurinsa, na tabbatar zai saurare mu, zai kuma yi maka uzuri." Sai a sannan Annur ya sauke ajiyar zuciya, yana jin sassauci a cikin zuciyarsa. "Kana ganin boka zai saurare mu gobe kuwa?" Ya ɗaga laɓɓansa ya furta a tsanake, yana shanye damuwarsa. "Na tabbatar ransa zai ɓaci, saboda yanda kuka yi cewa zai kashe ko wane aiki yau ya maka wannan aikin. Amma ba komai, zai saurare mu. Kawai dai ka zo da wuri mu tafi." "To zan zo, zan zo da sassafe Farouk. Good night." Sallama suka yi da juna sannan suka tsinke wayoyin nasu, ko wane da tunanin da yake saƙawa a zuciyarsa. Sai ma yanzu Bobby ya tuna cewa ɗazu sun yi da Maryama zai kira ta, sam! Ya shafa'a sai yanzu. Latsa kiran Maryama ya yi amma shiru bata ɗauka ba. Ya sake kira nan ma shiru, hakan ya sa ya mata text cewa ta yi haƙuri bai samu kiranta ba, uzururruka ne suka sha kansa. Ƙaramar ƙwalwa irin ta mashaya, sam! Ya kasa gane cewa Maryama ita ce suke neman ɗana wa tarko. Bai yi tunanin ga suna ya zo ɗaya ba, sannan kuma Annur ya shaida masa yana ta kiranta bata ɗauka ba, shi ma kuma ya kira bata ɗauka ba. Ajiye wayar ya yi kusa da shi, yana tsananin tausayawa abokinsa. Matuƙar wannan ƙullin ya warware, shi kanshi Bobby ɗin yana cikin matsala. Maryama kuwa ƙarfe sha biyu daidai alarm ɗinta ya buga. Tashi ta yi da miƙa ta miƙe zaune. Tana tunanin irin baccin da ta yi, kamar matatta, tun da ta kwanta bata farka ba sai yanzu. Tsaye ta miƙe kai tsaye ta nufi inda wayarta ke jikin chaji. Da ƙyar take buɗe idanuwan nata, har ta tarar da tarin missed calls ɗin da ke jere a allon wayar. "Ya Rabb!" Ta faɗa haɗe da dafe kai. "Ashe a silent na bar wayar nan, gashi na manta da Annur zai kira ni. Subhanallahi!" Ta matuƙar jin haushin hakan, damuwarta ma ɗaya plan ɗinsu da yake neman lalacewa. Kamar ta latsa kiransa, saboda kiran da ya mata ya fi ƙarfin talatin. Ga kuma na Jiddah, wanda aƙalla zasu kai uku ko huɗu. Sai na Bobby guda biyu, na wata lamba guda biyu. Rasa wanda zata fara kira ta yi, hakan ya sa kawai ta fasa, ta cire daga silent, sannan ta nufi ban ɗaki domin ɗauro alwala. Tun tana ciki ta fara jiyo kira a wayar, bata fito ba har sai da ta kammala alwalar duka, a lokacin wayar har ta tsinke an sake kira. Lambar Annur da ta yi saving da sunansa ta gani, hakan ya sa ta sauke ajiyar zuciya, haɗe da ɗaukar wayar. "Assalamu alaikum." Ta faɗa cikin sassanyar muryarta, wacce ke nunar da ta tashi daga barci. Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke, bai san sanda ya saki murmushi ba, yana mai matuƙar jin daɗin muryar tata. Tun bayan wayarsa da Bobby ya kasa barci, maimaita kiran Maryama kawai yake amma bai dace ba, sai yanzu da ya riga ya cire tsammani. "Maryama kina lafiya? I've been calling your number baki ɗauka, I hope all is well." "Zan iya sanin da wanda nake magana?" Ta furta cikin salon jan hankalinsa, dan ta tabbatar ba zai ɓoye mata ba, dole zai mata bayanin kansa. "Ye..yes, why not? Am Annur Iqra Al-Hussein. Na kira ki ne, akwai maganar da nake so mu yi." Gyara zamanta ta yi bayan ta zare wayar daga chaji, ba tare da tunanin komai ba ta ci gaba da saurarensa. "Ina fatan zaki bani aron lokacinki, ki saurari kalamaina, ki ji abin da nake tafe da shi. Amma fa sai kin daure, saboda abin da yawa, zai iya ɗaukarmu tsawon lokaci." "Ina saurarenka." Ta faɗa a hankali, ta ma cire tunanin karatun da zata yi, saboda a ganinta, wannan wata dama ce ta zo mata, wacce ta jima tana tsumayenta. "Maryama! Kin tashi kuwa?" Ta jiyo muryar Mamanta, tana tinkarowa ɗakinta. *** A inda take zaune ta haɗa kai da guiwa ta fara jiyo takun mutane. Daga kanta ta yi ta kalle su, Mahmouda ne da ƙannen nan nasa, suna mata kallon tuhuma, suna son sanin dalilin kukan da take yi. "Giɗe ba kuka zaki yi ba. Allah ne Ya ɗora mai wanga laluri, kuma shi zai yaye mai." Ɗaya daga cikinsu ta faɗa, tana jin tausayin Fiddou. Ta buɗe bakinta zata mata magana ke nan likita da nurse suka shigo, hannun nurse ɗin riƙe da takarda. "Giɗe ga reffer letter ɗinai nan. Ku ɗaukai ku kai asibitin gwamnati. Na kira abokina na sanar mai yanzu, ku tahi dai, Allah Ya bashi lahiya." Mahmouda ne ya karɓi takardar, yana son sanin dalilin yi ma Modu reffer ɗin. "Gata nan zata yi ma bayanin komai. Kai ina ganin hwa mun gama da kai, ina ƴan sandan nan suke? Su taho ka yi signing, dan ya warke da duk abin da ka damunshi wanda ya danganci banka tai da ka yi, sai ƴan raunukan da ba za a rasa ba.." Sauke ajiyar zuciya ya yi Mahmouda. Yana jin zuciyarsa ta samu sassauci, yanzu kam zai zauna zaman ta'aziyyyar mahaifiyarsa ba tare da tunanin komai ba. Sai dai kuma me? Yana tsananin tausayin Modu, gashi kuma bai san abin da yake damunsa ba. "Mun gode ƙwarai Dr. Ka taimaka muna ƙwarai da gaske, Allah Shi saka ma da alheri." Fiddou ta faɗa tana ƙoƙarin shanye hawayenta. "Babu komai ai. Allah Ya bashi lahiya, Allah Ya taƙaita abin." Amin suka amsa da shi su duka da ke wurin, kafin likitan ya juya, Mahmouda ya bi bayansa. Kun ga ɗan ƙaramin haukan da Annur ya yi ko? wai duk gudun kar ƙullinsa ya warware. Ya manta cewa dare dubu na ɓarawo, rana guda tal ta mai kaya. Duk irin mugun abun da mutum yake aikatawa, dole akwai ranar tonuwar asirinsa, akwai ranar dana sani, akwai lokacin da zai fallasa, kowa ma ya san da halinsa gaisuwa ta musamman gare ki Queen miemie. Jinjina da fatan alkhairi ga ƴan group ɗin Nagarta writers fans. Ina yinku irin totally ɗin nan, fi sabilillah. Kamar yanda na faɗa maku, ba kullum ne zaku ringa ji na ba, sai dai zan yi iya ƙoƙarina, dan ganin kuna samu akai akai. Thanks all. Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:49 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 3⃣5⃣ Cikin tsarguwa ta gaggauta janye wayar daga kunnuwanta, ba tare da ta kashe ba. Ƙoƙarin amsa kiran Maman tata take, sai dai tana gudun bincike irin na Mama, babu wuya za ta gano cikin halin da take. "Maryama kin tashi kuwa?" Ta sake jin muryar Mama, saboda bata riga ta kunna hasken ɗakin ba dama. "Ehh, ehh na tashi. Har alwala ma na yi Mama." "Ok masha Allah! A yi sallah kafin a fara karatun ko? Za ki fi jin daɗinsa sosai." "To." kawai ta faɗa haɗe da latsa switch na wayar, ta kashe ta baki ɗaya. Miƙewa ta yi tana jin kamar ƙafafuwanta ba za su iya ɗaukar gangar jikinta ba. Ko kaɗan ba ta yi tsammanin zuwan Mamanta a daidai wannan lokacin ba. Dafe kansa ya yi a daidai sanda yake jin kalaman Mama. Gabansa ne ya tsananta duka, yana tunanin yanda zai yi kuma. Sake kiranta ya yi amma ya ji a kashe, bai san sanda zazzafan hawaye ya fito masa ba, duk iya jarumtar dannesan da yake yi. "Shi kenan na san by now boka ya yi zuciya. Ya zan yi ne ni Annur? Am totally confused, I've no idea on what to do, help me out ya Allah!" Sallarta ta fara bisa kafet, tana mai ƙoƙarin cire rauni daga zuciyarta. Bayan ta gama ta hau karatu sosai, tana jin yanda natsuwa ke daɗa sauka ga duk ilahirin jiki da jininta. Lallai karatun Al'Qur'ani wani abu ne, wanda babu tamkarshi, wanda ke dakar da zuciyar mutum, yake saka natsuwa sosai a cikin zuciya. Ta jima tana karatun kafin ta sadaƙe, ta miƙe ta kawo raka'a biyu, a lokacin ƙarfe uku na dare kenan. Bayan ta gama ta yi addu'a sosai, ta ma iyayenta, sannan kuma ta kai kukanta wurin Allah, a kan wannan aiki da take son yi. Tana son Allah Ya taimaka mata, ya kawo mata mafita, kar wani abu ya faru da su har su gama. Kwanciya ta yi da addu'a a bakinta, ta tofa wa kaf ilahirin jikinta, da hijabi a jikinta bata cire ba, barci ya yi awon gaba da ita. Kwalbar codein ya fiddo daga cikin deep freezer ɗinsa, ya jijjiga ta sosai, sannan ya ɗaga kansa ya kwankwaɗe, yana son damuwar da ke cikin zuciyarsa ta kau. Sigari a fiddo daga lakar bed side nashi, ya bata wuta, sannan ya hau zuƙarta, yana yi hawaye na fita daga idanuwansa, hawayen neman mafita kawai, dan ya tabbatar matsala ta auku, babba ma ba ƙarama ba. Washe gari. Da ruwan sama aka tashi kamar da bakin ƙwarya. Tun bayan da aka kammala sallar asuba ruwan ya sauko, da ƙarfi sosai, irin mai haɗe da iska ɗin nan. Baccin safe take mai cike da jin daɗi. Tana jin daɗin baccin matuƙa, ko farkawa ba ta yi ba tun da ta yi sallah ta kwanta. A hankali ta fara buɗe idanuwanta, tana jin yanda zuciyarta ke mata rauni, wanda ta rasa dalilin hakan. Ta sani, duk sanda ake ruwan sama daɗi take ji a zuciyarta, tana son yanayin sosai, ba wai lallai sai tana barci ba, ko idonta biyu ma. Amma a wannan gaɓar, saɓanin haka take ji. Ga tsananin duka da zuciyar tata take yi, tana tuna abin da ya faru bayan ta gama sallar asuba. * Da ƙyar ta iya buɗe idanuwanta, saboda barcin da yake cikinsu, na tashin da ta yi. Miƙewa ta yi bisa kafafuwanta, tana hamma haɗe da miƙa, ta nufi hanyar banɗaki. Alwala ta ɗauro sannan ta hau bisa kafet, ta fara da raka'atainil fajr sannan ta yi sallar asuba, a lokacin ruwa ya fara saukowa a hankali, ana yayyafi, ga iska sosai ana yi. Bayan ta gama ta yi adhkar, sannan ta cire hijabin nata, ta haye bisa gado ta kwanta. Ta jawo bargo zata lulluɓa kenan ta ji fitsari take ji, hakan ya sa ta miƙe ta yo sannan ta dawo. Abin da ba ta saba yi ba kenan, ko kaɗan ba ta yarda ta kwanta ba tare da alawala ba, ko da kuwa bayan sallar asuba ne irin na yau. Gabanta ne ya faɗi, ta dafe zuciyarta, tana tunanin dalilin faruwar hakan, sai dai kuma ta gagara ganowa, take ta kawar da komai, ta haye gado ta kwanta abinta. Bakinta ta buɗe zata fara addu'a, sai hamma ta zo mata, ta ƙarisa salatin da take yi haɗe da hammar, sannan kawai ta juya ta ci gaba da baccinta. * Ƙoƙarin motsa hannunta ta yi amma sam! Ta kasa. Ta gwada ɗaga gangar jikinta nan ma ta kasa komai. Gabanta ne ya tsananta faɗuwa, ta fara tunanin abin da ya same ta, sai dai ta rasa gane komai, tunanin mummunan mafarkin da ta yi kawai take. Ƙyafcin ido kawai take iya aikata wa, daga ba shi ba kuwa, komai ta kasa yi, bakinta take so ta buɗe ta ƙwala wa mamanta kira ma ta kasa. A hankali ta fara jin wani nannauyar abu na fita daga cikin zuciyarta, yana saukowa har bisa gangar jikinta, tun daga bisa kanta ya ringa tafiya, har sai da ya iso bisa tafin ƙafarta. A daidai nan ne ya fice da ƙarfin gaske, ta ji wata irin azaba wacce tun da take a rayuwarta ba ta taɓa jin irin ta ba. Kamar an ɗauki garwashi an watsa mata a tafin ƙafar haka ta ji. Tun bayan fitar abun kuma ta ji ta koma daidai, hannun na ta ma ya ɗagu, sannan a hankali ta tashi zaune, tana tunanin abin da ya same ta. Ba ta san sanda hawaye mai zafi ya fara mata kwaranya ba. Hankalinta a tashe ta dafe ƙirjinta, ta runtse duka idanuwanta, tana karanto addu'a a bakinta. Sai a yanzu ma take tunanin abin da ya faru da asuba. Ashe fa ta manta babu alwala ta kwanta, saɓanin ko yaushe, yanda ta saba a rayuwarta ko bata sallah to ba dai ta kwanta ba ta da alwala ba. Addu'a sosai take yi, tana kuma samun natsuwa sosai, tana jin sassauci a cikin zuciyarta. "Assalamu alaikum." Muryar Muhammad ce ta saka ta buɗe idanuwanta, tana kallonsa cikin shiga mai kyau, ya saka farar shadda da baƙar hula. "Yaya Maryama lafiya na gan ki haka?" Ya faɗa yana bin ta da kallo, saboda yanayin da take ciki dole ne a fahimci ta yi rashin natsuwarta ne. "Uhmm...babu komai Hammad. Ba dai har ka shirya ba." "Na shirya Yaya Maryama. Ke kawai nake jira." "Ok ka koma a falo ka jira ni ina zuwa." "To." Kawai ya faɗa sannan ya fita, har ya ɓule daga ɗakin bai daina waiwayenta ba. Wanka ta shiga daga nan, a ranta tana tunanin halin da ta shiga yau. Lallai mai rai ba wata tsiya ba ne. Cikin lokaci kaɗan komai na ta ya juye, ta gagara ko da motsi. Yanzu fa idan mutuwa ce ma a haka za a ce ai an kwana da ita lafiya, aka wayi gari babu ita. A kasalance ta gama shirin. Ta saka baƙar abaya mai adon pink. Sannan ta ɗaura ɗankwalin a kanta, ta fiddo ƙaramin mayafi pink ta ɗora a bisa gado. Falo ta fito jikinta sukuku, sai ƙoƙari take dan ganin ta koma daidai amma hakan ya gagara. Fargaba ce haɗe da tsoron Allah mamaye a cikin zuciyarta. "Ina kwana Mama?" Ta faɗa da sassanyar muryarta, tana saita dubanta zuwa ga mahaifiyarta. "Lafiya ƙalau Maryama. Kin sha barci. Ai tun ɗazu Muhammad ke son zuwa ya tashe ki nake hana sa. Wai ya ƙagara ku tafi haka nan." "Ai fa dai na ga alama Mama. Tun da ga shi nan har ya shirya tun ɗazu. Allah dai Ya sa zakwaɗi ma ya bar shi ya karya." "Ya ci ƴar guntuwar doya. Kin ga sauran nan ya ƙulle a leda wai zai tafi ma Abdul-Ahad da ita." Dariya sosai Maryama ta kece da ita. Da gaske Muhammad ya bata dariya. Wato shi ya rasa ma abin da zai kai wa Abdul tsaraba sai soyayyar doya, wadda ta riga da ta gama hucewa. "Nawawo for this boy. Kai yanzu fi sabilillahi wannan doyar ce zaka kai ma ƙaninka tsaraba?" Matsowa ya yi kusa da ita yana murmushi. "To Yaya Maryama ai ya fi na je masa haka nan ko? Amma idan na kai masa doyar nan na tabbata zai ji daɗinta." Su dukansu dariya suke a wannan gaɓar, har shi kanshi Muhammad ɗin dariyar yake. Miƙewa ta yi za ta ɗauko kalacinta ta ji wayarta na ringing. Aunty Islam ta gani a rubuce, hakan ya sa ta koma ta ɗauki kiran da sallama a bakinta. Kusan mintinsu biyu suna waya, kafin ta juyo ga Mama ta ce, "Wai a gidansu zamu same su. An fara yi masu aikin gida ne yau, tun jiya da dare mijin ya ce kawai ta je can gida. Har kira na ma ta yi da wata lamba a cikin daren ban ɗauka ba. Ga shi nan za ta turo min address yanzu." Mama ta ce, "To ba damuwa ai. Sai ki hanzarta, na tabbata yanzu za ku ga Mallam Ado ya zo ɗaukar ku." Kitchen ta nufa ta zubo doya a plate, sannan ta ɗauko lemon 5 alive haɗe da cup a hannunta. Zama ta yi tana ci a hankali, fiye da rabin tunaninta yana ga abin da ya faru yanzu. Ta na son kiran Jiddah ta sanar da ita komai, sai dai kuma yanzu babu lokaci, dole sai idan sun dawo. Ba ta gama ci ba Mallam Ado ya yi sallama. Yana Shaida masu cewa ya iso, su same sa a waje. Tashi ta yi ta mayar da kayan kitchen, sannan ta shiga ɗaki ta yafa mayafinta ta fesa body spray ta fito. Bankwana su ka yi wa Mama, sannan su ka fice daga gidan, zuciyar Muhammad sayau take, yana tsananin jin daɗin ziyarar da za su kai ma Abdul. *** Annur kuwa tun da sassafe ya shirya cikin ƙananan kaya ya fita, ko sallama bai tsaya ya yi ma Momy ba kawai ya kama hanyar gidan su Farouk Sardauna. Kiran Bobby ɗin ya yi a waya, bai ko tsaya ya ɗauka ba ya fito, dan ya san dalilin kiran nasa. Buɗe motar ya yi ya zauna a gaba sannan ya rufe. Ya kalli yanayin abokin nasa, yanda duk ya bi ya susuce a cikin ƙanƙanin lokaci. "Annur wannan fa damuwar da ka saka kanka a ciki sam! Ba ita ce mafita ba. Dolenka ka zama jarumi, ka ƙoƙarta mayar da komai ba komai ba, sannan walwalarka za ta dawo. Amma idan kana cikin wannan halin, ba ka tsammanin su Momy za su iya fahimtar wani abu? Lallai dole za su fahimta." Duk da tuƙi yake amma hakan bai hana shi kallon Bobby ba. Ɗan lumshe idanuwansa ya yi, sannan ya mayar da kallon na shi ga tuƙinsa, ya ce, "Duk yanda zan yi dan ganin na kawar da wannan damuwar na kasa. Haka kawai nake jin gabana na faɗuwa, kamar komai ya kusa dagule wa. Ina fargabar haɗuwarmu da boka, dan ba ni da hujjar da zan kare kaina a wurinsa." Ajiyar zuciya ya sauke Bobby, a tsanake ya ce, "Haka ne. Amma kuma ai dole ya maka uzuri. Shi kansa da yake aiki da tsafi tun farko ya ce yarinyar ta gagae shi, bare kuma kai da ba ka taki komai ba?" "Haka ne Farouk. Maryama kam ta yi nisa ba ta jin kira. Ta riƙa sosai a ibada, ban kuma ga abin da zai iya dakatar da ita ba." "Ina ga kawai abin da ya kamata, idan da yanda zai yi ya canza salon aikin baki ɗaya sai ya taimaka mana. Wannan dokar ta true love gaskiya dole a karya ta, saboda fa zuciya ba ta da ƙashi. Ba ka isa ka tanƙwara ta a kan abin da ta gani tana so ba." Da wannan firarrakin suka isa wurin bokan. Kai tsaye suka zarce tare da aikata duk yanda su ka saba idan sun je wurinsa. Zama suka yi a ƙasa, Bobby ya masa kirari sai ga shi ya ɓullo, yana kallonsu su duka biyun. Murmushi ya saki da ƙarfin gaske. Ya dunƙule hannuwansa duka biyun sannan ya buɗe su. "Ka yi aiki mai kyau, ban taɓa tsammanin yiuwar aikin nan ba. Daga farko na ji haushinka sosai, saboda wahalar da ka ba ni, kuma a banza. Sai dai na daure a ƙarshe, sai ga shi kuma mun yi nasara." Ido buɗe suka kalli junansu, suna matuƙar mamakin kalamansa. Su da su ka yi zaton zai balbale su da masifa, amma sai su ka ji akasin hakan, hasali ma yabo ne ya fito daga bakinsa. Page din nan ya ba ni wahala. Sai da na rubuta fiye da rabi ya goge😭 da ƙyar na samu maimaita shi. Amma duk da hakan dai ya sha banban da na farkon. Thanks my fans, ina jin daɗin yanda kuke bibiyata. Saƙon ta'aziyya ga masoya Irfan. Ina mai taya mu jaje na rashin jarumin labarin MH da mu ka yi😧 na sha kuka kamar ba gobe, har nake jin mutuwar kamar da gaske ne ta faru. Sai dai kuma ba abun mamaki ba ne, saboda mutuwa ko kalmarta kawai ka ji wani tashin hankalin ne. Fatanmu dai Allah Ya sa mu yi kyakkyawan ƴarshe, ya kyautata makwancinmu. Ina jajen ƙawata XARAH BB. Ban san ina kika shige ba, ta yiu kuma ɗan Baba ne ya ɓoye mana ke.😂 Allah Ya bada lafiya amin. Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:50 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 3⃣6⃣ Assalamu alaikum. Na samu ƙorafi daga wasu cewa; wai duk karatun da Maryama ta yi kuma sai asiri ya kama ta? Abin da nake so ku gane shi ne; a duk duniya babu mutum sama da manzon Allah, (SAW). Shi ne mafi daraja, ma fi soyuwa ga Allah Maɗaukakin Sarki! Shi ne wanda ya fi kowa ilimi, kuma ya fi kowa aiki da shi. Shi ne wanda ya fi kowa ibada, kuma yake kiyayewa. To kuma asiri ya kama shi. Shin mu waye da asiri zai gagara kama mu? Shin Maryama wace iriyar mutum ce, wacce asiri zai gagara kama ta? Kar ku manta, an jima ana ƙoƙarta asirin ya kama ta, amma ya gagara shigarta, saboda kariya. To lokaci ɗaya kuma Allah Ya jarrabe ta, Ya shagaltar da ita, sam! Ta gagara yin abin da ta saba yi. Kenan dai ba abun mamaki ba ne dan asiri ya kama ta. Masu wannan tunanin, ku yi haƙuri ku zuba min ido. Ni na san kan labarina, na kuma san yanda ya kamata. Please and please, ku zuba min ido kawai, ku dai aikinku karatu ne. Ku bari har sanda na kammala, duk mai ƙorafi ƙofa a buɗe take. A daidai lokacin an ga yanda ƙarshensa zai yi kenan. Fatan za a fahimce ni. Wanda na ɓata wa ya yi haƙuri. *** Cikin ɗaga sauti bokan ya ce, "A yanzu kam an gama komai. Duk wata damuwa ta ka ta ƙare Annur, saboda an samu nasara a kan yarinyar, duka soyayyar da kake mata an fitar, aiki kuwa zai gyaru sosai yanzu." Murmushi suka saki su duka biyun a tare, duk da ba su san dalilin faruwar hakan ba, sai dai su na ji a jikinsu akwai dalili. "Ku ajje abin da za ku ajje, ku tafi, an kammala da aikinku. Ina mai tabbatar ma ku da cewa asirinku ba zai taɓa tonuwa ba. Wannan ɓoyayyen al'amarin ba zai taɓa fallasuwa ba." Kuɗi ya ciro daga aljihunsa Annur, ya dire su a gaban boka, sannan suka miƙe su duka biyun, suka nufi barin gidan. A mota har rige rigen magana suke, Annur ya ce, "Ko ta ya wannan aikin ya faru?" "Tambayar da ke cikin zuciyata kenan. Amma dai wannan ba shi yake gabanmu ba. Fatanmu dai aiki ya yi, kuma ya yi ɗin. Faƙat." Hannu suka haɗa suka tafa da ƙarfi, duk wanda zai kalle su zai tabbatar da tsantsar farin cikin da suke cikinsa. *** Tun daga sanda aka ba Fiddou reffer letter take rusar kuka. Tana son zuwa gidansu ko dan a ji daga gare ta, amma kuma ba ta son tafiya ko yaya ta bar Modu. Tun washe garin da suke asibiti ta je gida ta ɗauko kaya, ba ta sake komawa ba. Yayanta dama ya yi tafiya, matsarsa ce kawai, kuma ba ta damu da ita ba bare har ta nemi jin halin da take ciki. Tagumi ta buga a bisa teburin da take zaune, sai Modu kwance suna jiran likita. Kimanin awarsu biyu kenan a asibitin, sai dai da yake asibitin gwmanati ce, akwai layi sosai, dole sai sun bi har a zo kansu. Ita babban tsoronta ma kar Modu ya farka, dan ba ta san yanda za ta yi da shi ba. Da haka har aka zo kansu. Irin kujerar ɗaukar marar lafiyar nan ce ta yi magana aka zo da ita, mutum biyu su ka cicciɓa Modu suka zaunar a ciki, sannan su ka tura shi har cikin Ofishin likitan. Zama ta yi bisa kujera tana fuskantar likitan, damuwa ce danƙare a cikin zuciyarta, tana ƙoƙarta danne hawayen da ke fita daga idanuwanta. "What's his problem?" Muryar likitan ta dawo da ita hayyacinta. Takarda ta miƙa masa, ta ce, "Mu ne Dr. Huzaif yat turo daga Amana clinic. Ga takarda tai nan." Karɓa ya yi likitan yana dubanta, ya ce, "Mi da ba ki shigo ba tun ɗazu? Ai ban san kun iso ba giɗe." Shiru ta yi bayan ta sadda kanta ƙasa, dan ba ta ji ko kaɗan tana da ra'ayin yin doguwar magana. Damuwar halin da Modu yake ciki kawai ta ishe ta. Ga kuma zullumin abin da zai faru. "Gado za a ba shi." Ya faɗa bayan ya ajje takardar bisa teburinsa. Ya ɗauko abin awon zuciya ya ɗora a saitin zuciyar Modu, yana jin yanda ba ta tafiya yanda ya kamata. "Giɗe na cikin matsala mai girma. Ina gudun kar zuciya tai ta mutu, wato ta tsaya cak!..." Yana neman ci gaba da magana Fiddou ta dakatar da shi da hannu. "Halan wane irin likita kake? Mi da ba ka san irin maganar da za ka hwaɗi ma mutane ba? Yanzu idan aka yi gawa biyu hwa? Ba ka gudun maganar da kai yi tana iya tsaida bugun zuciyata? Halan ka san irin darajar da Modu gare shi a cikin zuciyata?" Kuka sosai ya ci ƙarfinta. Kalaman likitan take ji suna ratsa duk wata gaɓa ta jikinta. Tsoro take kar maganarsa ta tabbata. "Haba i haƙuri giɗe!" Ya faɗa yana murmushi, kamar ma bai damu da munanan kalaman da Fiddou ta jefa masa ba. "Kwantar da hankalinki ke jiya. I'll try my best dan ganin giɗen ga ya samu lahiya. Likitan zuciya nike, na miki alƙawarin ba shi kulawa iya ƙarhina." Sai a sannan ta ɗan samu sassauci, amma duk da hakan ba ta daina yin kuka ba. Nurses ya kira cewa su ba Modu ɗaki, kuma Amenity za a ba shi, saboda mutum mai matsalar zuciya ba ya son wurin da za a yawaita hayaniya, ko kuma mai cinkoso da yawa. Bin bayansu ta yi Fiddou, a daidai wannan lokacin ta daina kukan, sai dai kukan zuci kawai take, wanda da shi ta gwammaci tai ta yin mai ƙarfi. Gyare yake ɗakin tsaf, su na shiga wani lebourer ya shigo da bed sheet da pillow case, ya shimfiɗa a gadon, sannan aka kwantar da Modu a kai. Bayan sun bar ɗakin ne aka bar ta daga ita sai Modu. Hakan ya sa ta tashi ta ɗan rufe shi da blanket, sannan ta fara haramar tafiya gida. Ta Offlishin likita ta fara biyawa, ta shaida masa cewa za ta je gida, idan akwai wani abu da ake buƙata sai a rubuta mata yanzu kafin ta tafi. Babu komai ya shaida mata. Yanzu jiran farkawarsa kawai yake, saboda akwai abin da yake son ji daga gare shi. "Dr. Ya na da taɓin hankali hwa. Halan mi za ka ji daga garai?" Ta faɗa cikin muryar tausayi. "Duk da haka akwai dabarar da zan ringa yi mai, sannu a hankali za mu yi shaƙuwar da da kai nai zai hwaɗa min damuwa tai." Shanye kukanta ta yi, ta ce, "To shi kenan likita. Ina hwatar hakan. Bari in tai." Har ta juya za ta bar ofishin ta jiyo muryarsa ya ce, "Ba ki ji ba." Ta juyo da kallonta gare shi, tana jiran abin da zai faɗa. "To idan kin tahi kin bar shi shi ɗai, halan wa zai hwaɗi min idan ya tashi?" Shiru ta ɗan yi jim! Kafin ta ce, "Ba daɗewa zan yi ba likita. Na jima ban tai gida ba. Ina da buƙatar in koma su gan ni in gan su. Minti arba'in ya ishe ni." Kai kawai ya jinjina ba tare da ya ce komai ba, ta kama hanya ta bar ɗakin. Kai tsaye gida ta nufa, ko kuɗin abun hawa babu a tare da ita, ta hau ne dai kawai komai ta fanjama, fanjam! Idan kuma zai haƙura ta shiga gida ta ɗauko masa to. A ƙofar gida mai mashin ɗin ya dakata. Bayan ta sauka ta ce da shi ya mata haƙuri ta shiga gida ta fito, za ta sallame shi. Babu ko musu ta tafi ta bar shi, bayan ya faka mashin ɗinsa. Sumi sumi ta shiga gidan, hankalinta a tashe, dan ba ta san kalar masifar da za ta tarar ba. Sallama ta yi ƙasa ƙasa, tana bin mutanen da suke cikin gidan da kallo. Babu wacce ta amsa sai mutum ɗaya, wadda har da fara'a a fuskarta ta iso ta rungumi Fiddou. Ita ma Fiddou rungumar tata ta yi, tana faɗin, "Hadiza halan yaushe kika zo?" Kafin Hadizar ta yi magana ta jiyo muryar matar yayanta ta ce, "Tun sanda kika tahi wurin yawon iskancinki. Ke Fiddou bari ki ji in hwaɗi miki, na gaji da wanga iskanci naki, wanda kullum babu sauyi sai ma ci gaba da yake. Dan dai kin ga Yayanki ba shi nan ne hwa. Waton idan ya zo ya ce na bar ki kina hita yawon karuwanci ko? To walle ba ki isa ba!" Wata budurwa da ke gefenta ta ce, "Salon jan sharri ne kawai. Waton idan ya tashi ya ce ke kina harkar bikin gidanku, kin bar ta ita kuma tana biɗiɗinta. Makira ana magana tana bin mutane da idanuwa kamar warinta." Wata mata ta buɗe baki ita ma za ta tofa na ta albarkacin bakin kenan Hadiza ta ce, "Wai me ke damunku ne dan Allah? Wannan wane irin hali ne? Daga dawowarta babu ko maganar arziƙi kawai sai mugayen kalamai? Ku za ku so a muku haka ne? Ni fa ba na son haka gaskiya." "Inye! Lallai ma Hadiza. Ni hwa ba na son wanga hali kuma ke sani. Ke a dole wayayya wadda ta je Katsina. To walle ba za mu ƙyale giɗe ba. Dole ne mu hwaɗi ta yi iskanci." Kuka sosai Fiddou ta fasa. Tana matuƙar jin haushin kalmar da matar yayanta ke yawan jifanta da ita. Wai ita ce ƴar iska. Ga ƙanwarta nan Hadiza, wadda tsabar yawon bariki ya sa ma ta bar garinsu, ta koma Katsina da zama. Amma ba su ga nata ba, sai ita da ke ƙoƙarta kare mutuncin kanta a ko da yaushe. A cikin kukan ne ta tuna da mai mashin da ba ta sallama ba. Da sauri ta bar wurinsu, ta nufi ɗakinta. A cikin lakarta ta fiddo ƴan kuɗaɗen da take ajiya, ta zari daidai wanda za ta sallami mai mashin ɗin, sannan ta fito domin ta kai masa. Fizgo ta ta yi matar yayanta, ta matse mata kafaɗa da ƙarfi, tana binta da wani wawan kallo. "Dan Allah dai Aunty Sahiya ki rabu da ni. Ki ƙyale ni." "Na ƙi in ƙyale ki Fiddou. Waton in sake ki ki koma wurin iskancin na ki ko?" Cikin jarumta ta fizge jikinta, a hanzarce ta fita daga gidan, ta bar su sake da baki. Bayan ta sallame shi ta dawo. Tana jin yanda tsoron Aunty ke fice mata daga zuciya. Ita fa in dai kan Modu ne, to za ta iya jure komai, wulaƙanci da kyara, matuƙar dai ba zai cutu ba. Tana shiga Aunty ta jawo hannunta da masifa. Ba ta ankara ba Hadiza ta janye Fiddou da fushi sosai, ta ce, "Wallahi ba ki isa ba! Wai me ya sa ba ku da imani ne? Yarinya marainiya amma babu imani sai a ringa cutar da ita? Wuce mu tafi Fiddausi." Ɗakin Fiddou ɗin suka nufa, Fiddou sai kuka take, Hadiza na rarrasarta. "Fiddou in dai ba za ki fitar da tsoronsu ba wallahi a haka za ki ci gaba da rayuwa. Yo wannan rayuwar ko naka na jikinka wa ya ce miki ana gwada tsoronsa a fili? Ai sai ya raina ki. To bare kuma matar yaya. Me ake ci da matar yaya ko ta ƙwarai ce bare kuma muguwa kamar Aunty Safiya?" "Ban san yanda zan yi ba Hadiza. Ina cikin matsala. Aunty Sahiya ta kasa ganewa. Ta ƙi ta bar ni da damuwad da ac cikin zuciyata. Ga Modu can kwance ba lahiya. Ni ban ma san inda zan dosa ba. Rana zahi inuwa ƙuna!" Kuka sosai take a wannan gaɓar. Tana ƙara tuna halin da ta baro Modu a ciki. "Yi haƙuri ya isa haka to. Yanzu ki samu ki yi wanka mu je na siya miki abinci, dan nan gidan dai babu komai, idan ma akwai na tabbata masifaffun can ba za su bar ki ki ci ba." Nufar yin wankan kuwa ta yi Fiddou. Kafin ta fito har kaya Hadiza ta fiddo ta ajiye mata. Tana jiran fitowarta. Bayan ta shirya suka kama hanyar fita. Ko kallon inda su Aunty suke ba su yi ba. Saboda Hadiza na ƙoƙarin fitar da shakku da fargabar Aunty Sahiya da Fiddou ke yi. Kai tsaye wurin sayar da abinci suka nufa. Siya suka yi suka ci, sannan Hadiza ta sa a ma Modu take away su tafin masa da shi. Bayan Hadiza ta biya kuɗin suka fito. Mashin suka tara ko wace ta hau ɗaya, kai tsaye suka nufi asibitin da Modu yake. Fiddou ce a gaba sai Hadiza bayanta, har suka shiga cikin ɗakin Modu. Modu suka samu a zaune, hannunsa ɗaya dafe da ƙirjinsa, ɗayan kuma a cikin bakinsa, yana tsotsar duka yatsun hannun. Dariya ya saki da ƙarfi a lokacin da ya haɗa ido da Fiddou. Ya yi yunƙurin miƙewa amma kansa ya sara masa, dolensa ya runtse ido, ya dafe kan nasa. Ledar hannunta ta saki Hadiza a lokacin da ta haɗa ido da Modu. Ta zaro duka idanuwan nata. Hannunta bisa kai tana bin sa da kallo. Kallon mamaki Fiddou ta bi ta da shi. Saboda yanayin kallon da Hadiza ke bin Modu da shi, da alama ta san shi ne. "Hadiza, halan lahiya?" Kai Hadiza ta gyaɗa har yanzu ba ta ɗauke idanuwanta daga gare shi ba. Hannunta na dama ta miƙe daidai saitinshi. Ta ringa gwada shi da yatsarta manuniya, bakinta na ƙoƙarin furta magana amma ya kasa. Da ƙyar ta iya ɗaga laɓɓanta ta yi magana, wanda idan ba ka kalli bakin nata ba ba za ka taɓa cewa ta yi magana ba. "Annur!" Ta faɗi a daidai isowarta gaban Modu. To masu karatu. An zo wurin ko? Na san haka wasu za su faɗi,😁 indeed, an zo wurin. Tighten your belts readers, sannu a hankali mun fara isowa wurin, wurin da nake yawaita faɗa maku za a zo. Akwai gwagwarmaya, akwai kuma sarƙaƙiya. Thanks all. Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:50 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 3⃣7⃣ follow me on wattpad @PrincessAmrah *** "Annur!?" Fiddou ta maimaita a bayyane, tana sake bin Hadiza da kallon tuhuma. "Kin san shi ne halan?" Ta jefo wa Hadiza tambaya, bayan ita ɗin ma ta ƙarisa a gabansu. "Annur me ya kawo ka nan? In ce ko jiyan nan muka rabu da kai lafiyarka lau? Na shiga uku! Hadiza ba dai shi ne mahaukacin da kika ba ni labarinshi ba ko? Wallahi wannan Annur ne." Duka a jere ta sako wannan maganganun, zuciyarta na ƙara tabbatar mata da cewa lallai wannan Annur ne ta gani, Annur ne zaune a gabanta. "Wace irin magana kike yi halan giɗe? Wane irin ko jiya ke ganai bayan kuma Modu gashi ya ɗauki kwanaki a asibiti? Shekararsa kusan uku a Maraɗi hwa. Kallarsa da kyau dai Hadiza. Ƙila dai ya yi miki kama da wanda kika magana ne." Hannunta ta sa ta fiddo yatsun Modu da suke cikin bakinsa. Ta ɗora su a bisa tafin hannunta. Idonta cikin nashi ta ce, "Annur ka fito fili ka faɗa mata gaskiya. Da alama dai wani mugun abun ka ƙulla shi ne ka yo nan a shekaran jiya rabuwata da kai kawai. Ka faɗa mata gaskiya na ce Annur!" Kallonta kawai yake yana yaƙe baki. Shi kanshi bai san dalilin shigarsa nishaɗin ba, kawai daga jin ta ambata masa sunan da ba nashi ba. "Ka daina wannan dariyar yaƙen Annur. Wallahi kai ne, na tabbata. Wace irin rayuwa ce ka jefa kanka a cikin kwanaki biyu kacal?" Har a lokacin Fiddou ba ta daina kallonta ba. Ba kuma ta sake furta mata komai ba. Sallamar Dr. Huzaif suka ji, sai nurse biye da shi ta riƙo file ɗinshi. Amsa sallamar ta yi Fiddou, har a lokacin ba ta daina mamakin kalaman da suke fitowa daga bakin Hadiza ba. Bayan Dr. Huzaif ya ƙariso inda suke ya ce, "Fiddou ba haka muka yi da ke ba. Kin san dalilin da yas sa na ce kar a kai Modu male ward, dan dai kar a damai da hayaniya. Sannan ko da za ki tahi gida sai da nis so in hana miki tahiya, saboda idan Modu ya tashi ki hwaɗi min. Amma abun mamaki sai ga shi har ya tashi ba ki taho kin hwaɗi min ba, sai nurse ce ta zo gittawa taj ji abin da ke hwaruwa. Sannan kuma ga hayaniya kuna yi, bayan matsalar zuciyar da giɗe ag garai." Sosai Hadiza ke binsa da kallo. 'Matsalar zuciya?' Ta tambayi kanta, bayan ta sake mayar da dubanta ga Modu. Ita ba ma ciwon zuciyar ne ya fi ɗaure mata kai ba. Yanayin nasa ne babban abun dubawa. Kayan jikinsa da sumar kanshi, haƙoransa da tun ɗazu yake yaƙewa duka abun mamaki ne. Ba ta gama mamaki ba ta jiyo muryar Dr. Huzaif ya ci gaba da magana. "Bari in sake hwaɗi miki maganar ɗazun nan wadda ba ta yi miki daɗi ba. Wallahi giɗe da kike gani ga shi ya kusa mutuwa. Zuciya tai tana daf da tsayawa, ta daina aiki baki ɗaya. Matuƙar ba ki kiyaye sharuɗɗa ba, to ki tabbata ya mutu kawai." Yana kaiwa nan ya ƙariso gaban Modu, yana kallonsa da murmushi sosai, haka shi ma Modu ɗin murmushi yake ma Dr. Huzaif. Mamaki fal a fuskar Hadiza. Wai da gaske Annur ya haukace? Kuma yana da ciwon zuciya, har ma za ta iya zama ajalinsa? Hawaye ta ji suna zarya bisa kumatunta. Tausayinsa take. Duk da ta san cewa rayuwar bariki ce suke yi da Annur, amma fa tana ƙaunarsa. Tana masa soyayyar da tun da take a rayuwarta ba ta taɓa yi wa wani ɗa namiji irinta ba. Sai dai kuma ta san a banza, tun da shi ba irin son da yake mata ba kenan. Jikinta kawai yake so, kawai ya biya ta kuɗi bayan ya samu biyan buƙatar kansa. Wayarta ta zaro daga cikin jakarta. Gabanta na tsananta duka ta nemi lambar Annur ta kira sa. Abun da ya daɗa tayar mata da hankali shi ne ƙin ɗaukar wayar da ya yi. Har kusan sau biyar tana maimaita kiransa amma ba aauka ba. Hakan ya tabbatar mata da tunaninta. Lallai wannan Annur ne, Annur da ta rabu da shi kwanaki biyu da suka gabata. Shi ɗin dai ne a gabanta yanzu, a matsayin mahaukaci kuma mai lalurin ciwon zuciya. Ba ta ko sake kallon inda Fiddou take ba a guje ta bar ɗakin, tana jin zuciyarta kamar za ta fashe. Hankalinta ya matuƙar tashi. Lallai dole ne a gare ta ta koma Katsina yau, kuma yanzu ma, domin ta sanar da iyayensa halin da ake ciki. Dole ta sanar masu, saboda su ƙoƙarta sama masa lafiya. Ta tabbatar har ƙasar waje ma za su iya fitar da shi, saboda mahaifinsa mai dukiya ne, dukiyar da za ta iya siyan duk wani abun siya, ciki kuwa har da fita wata ƙasa domin nemawa tilon ɗansa lafiya. Takowa ta yi Fiddou jiki sanyaye za ta bi bayanta, tana son sanin abubuwan da suke fitowa daga bakin Hadiza. Tana son tabbatar da gaskiyar lamarin. Wata ƙila ko ƙarshen wahalar Modu ce ta yi. Ƙila ko tana da masaniya da asalinsa ne. Sai dai kuma abin da ya ɗaure mata kai, jin ta ambaci shekaranjiya ma wai ta ganshi, alamun dai rashin ingancin zancen kenan. Kafin ta isa ƙofa ta jiyo muryar Dr. Huzaif ya ce, "Giɗe a samo ma abokina abinci ya ci." Sai a lokacin ma ta tuna da ledar abincin Modu da Hadiza ta saki tsabar mamaki. Fasa fitar ta yi ta dawo. Ledar ta ɗauko daga ƙasa, har miyar shinkafar ta ɗan fara zuba cikin ledar, mai duk ya gama tsiyayewa. Bayan ta buɗe ta motsa masa, tana ƙoƙarin zama a bakin gado ta bashi amma likita ya karɓa, ya ce shi zai ba shi da kansa. "Abokina Modu. Kai ɗan gata kake hwa. Ka ga abinci ma da kaina zan ba ka." Bai furta komai ba sai wannan yaƙe da ya zame masa abun yi ya yi. Sai lokaci zuwa lokaci yake ɗan dafe ƙirjinsa, ta gefen da zuciyarsa take. "Uhmm...abokina, ba ka bani labari ba." Shiru ya yi daga nan yana kallon yanda Modu ke ciccije bakinsa, hannunsa dafe da zuciyarsa, hawaye na ƙoƙarin fitowa daga idanuwansa. "Sannu ka ji Modu. Jarumi ba ya kuka saboda wani ciwo. Kar ka ba ni kunya do Allah de." Ya ƙirƙiro murmushi duk da tausayin Modu da ke cikin zuciyarsa. Murmushin ya yi shi ma Modu, hawaye kuma ba su daina fita daga idanuwansa ba. "Labarin Anrah nika son ka ba ni. Halan...?" Bai ƙarisa maganarsa ba Annur ya sake dafe ƙirjinsa, hawaye na tsananta fito masa. Da ƙyar ya iya ɗaga laɓɓansa, cike da ƙarfin hali ya ce, "Amrah!" Haɗe da fasa kuka da ƙarfi, ya buɗe duka muryarsa. Cike da tausayi Dr. Huzaif ya ajje robar abincin a gefensa. Ya yunƙura tashi ya hau bisa gadon. Kama Modu ya yi ya kwantar a hankali, yana tunanin ta inda zai ɓullowa lamarin. Lallai wannan Amrar ba ta rasa nasaba da matsalar zuciyar Modu, har ma da taɓin ƙwalwarsa. Ya ma rasa yanda zai yi da Modu a daidai wannan lokacin. Ba ya son ya masa allurar barcin nan, dan ya kula jininsa bai da ƙarfi sosai, tana jimawa ba ta sake shi ba. A daidai wannan lokacin kuma ba barcin Modu aka fi buƙata ba. Dole sai yana farke ko zai samu sauƙin hanyar kawo waraka ga Modu. Dafe kansa ya yi bayan ya koma ya zauna. Yana kallon yanda Modu ke riƙe da ƙirjinsa da duka hannuwan nasa biyu. Ya ciccije laɓɓansa sai faman gyaɗa kanshi yake. "Dr. Do Allah de ka ƙyale shi da maganar wagga Amrah. Da alama ba ya son maganarta ne." Fiddou ta jefo masa wannan maganar tana mai cike da jin haushinsa. Saboda ita fa babu abin da zai yi ya burge ta. Tun da ta kula da imaninsa ragagge ne, ga uwa uba rashin iya magana. Banza ya mata bai kula ta ba, sai murmushi da ya ƙirƙiro ya ce, "Amrah na nan tana jiranka Modu. Babban burinta shi ne ka koma gare ta, ku ci gaba da rayuwarku tare, ta ƙaunace ka, kai ma ka ƙaunace ta." Ɗago kanshi ya yi da murmushi ya kalli likitan, hawayenshi na shiga har cikin bakinsa ya ce, "Da gaske...Amrah...Amrah nake so!" "Na sani ai Modu." Dr. Huzaif ya faɗa da murmushi. Yana mai jin yaƙini a ranshi, lallai da alama za su yi nasara. "Amrah nake so! An ce wai ta tafi ta bar ni. Na san kuma ba za ta tafi ba, saboda komai na mu tare yake tafiya." Ido buɗe likitan ke kallon Modu. Mamaki ƙarara a fuskarsa. Bai taɓa tsammanin jin wannan kalamin daga bakinsa ba. Kamar dai mai hankali? A yanayinsa da komai da ya yi maganar, babu wanda zai ce marar hankali ne. Sai dai kuma bayan ya gama maganar, ya tabbatar masu da cewa lallai mahaukacin ne kuwa. "A tona rami zurun zurun a binne ni. Sai a ɗauko ta a saka a ciki. A rufe mu da ƙasa mu yita soyayyarmu a ciki ko?" Ga tausayi, ga kuma dariya. Har ga Allah Ya bashi dariya sosai wannan maganar da ya yi. Murmushi ya yi haɗe da faɗin, "hakan za a yi kuwa Modu. Ai ni ka ganni nan? Farin cikinka nake so. Dan haka dole zan kai ka inda take, musamman ma idan ka natsu, ka kuma zama abokina." "Da gaske kake? Na yarda. Mu ƙulla ma daga yanzu. Mun zama abokai." Ya yaƙe haƙora bayan ya miƙowa Dr. Huzaif hannunsa. Shi ma nashi hannun ya bashi suka dunƙule alamun yarjejeniya. Suna sakarwa junansu murmushi. Fiddou da ke tsaye dai hankalinta a rabe yake. Ga tunanin Modu da tausayin halin da yake ciki, ga kuma tunanin maganganun da Hadiza ta yi. A ƙarshe kuma ta tafi da gudu. Zama ta yi a ƙasa dirshan, hawaye na fita daga idanuwanta. Wannan wace irin jarrabta ce take cikinta? Tana fatan Allah Ya ba ta ikon cinye wannan jarabawa. Allah kuma Ya kawo ranar da Modu zai warke tas, ta miƙa shi ga danginsa. Tsayawa ta yi da zancen zucin a daidai wannan lokacin, haushin kanta kuma take ji. Ta miƙa shi ga danginsa ita kuma fa? Shin za ta iya ci gaba da rayuwa ba tare da Modu a kusa da ita ba? Za ta iya auren wani namiji baya ga Modu? Gyaɗa kanta ta yi kuma, tana jin wasu sabbin hawayen suna zarya a kumatunta. To idan ya warke kuma ya nunar da bai santa ba fa? Tabbas duk wata shaƙuwa da suka yi a yanzu ta banza ce, tunda ba a cikin hankalinsa yake ba. A haka ma da bashi da hankalin kodayaushe cikin ambatar Amrah yake, ina ga ya warke? Ta tabbatar aikin banza take. Dakon son banza take yi, tunda bai ma san tana yi ba. *** Tun bayan da suka dawo daga wurin boka bai nufi zuwa wurin aikinsa ba, sai gidan su Farouk Sardauna da suka wuce, domin sharholiyarsu, na nasara da suka samu. Zaune suke bayan sun yi mankas, suna ta zuƙar shisha, hankalinsu a kwance. Bayan gama shan shishar kuma sai barci ya ɗauke su su duka biyun, ba su farka ba sai kusan ƙarfe uku na rana, shi ma sai da mai aiki ta shigo ta kawo wa Bobby abinci ta masu knocking. Abincin ya karɓa Bobby, sannan ya rufe ƙofar ya fara ƙoƙarin tashin Annur daga barci. Bayan ya tashi ne wayarsa ta hau ruri. "Babe" ya gani a bayyane, hakan ya sa shi sakin tsaki, haɗe da mayar da wayar a silent. "Abokina tashi ga abinci an kawo. Na san shishar nan ta gama zazzage maka ciki, dama kuma ko abincin kirki ba ka samu ka ci da safe ba, ban ma ce ka ci komai ba." Gyaɗa kai ya yi Annur. Ya ce, "Wallahi kuwa guy. Ina wannan zullumin ta ya zan iya sakawa cikina wani abu?" Suka kece da dariya su duka biyun. Yana kallo har sau biyar Hadiza na kiransa amma ya ƙi ɗauka. Bobby ya ce, "Wai abokina ba babe ba ce ke kiranka?" Yatsine fuska ya yi Annur, ya ce, "Ita ce fa. Ban san kuma me take so da ni ba. Shekaranjiya ta sa na tura mata kuɗi wai za ta je biki Maraɗi. Ga shi kuma yanzu tana sake kirana, kuma ma da lambarta ta Nijar, alamun dai ba ta dawo ba kenan. Na tabbatar wasu kuɗin za ta nema, ni kuma na gama da ita. Kai wallahi ka san, wannan ɗin ma ba a banza ba. Na faɗa mata sai na fanshe abuna." Suka sake saka dariya su dukansu a daidai nan. *** "Ya kamata dai mu fara haramar tafiya gida haka nan. Ai mun sha yini." Maryama ta saki murmushi bayan ta yi wannan maganar. "Ke ɗin wa ku tafi tun yanzu? Ko fa la'asar ba a yi ba. Yinin da za ku mana kenan?" Dr. Islam ta jefo mata wannan tambayar. "Aunty Islam ai na ga ya kamata mu tafi haka nan." "To ba yanzu ba. Sai magrib ko kuna barin nan. Ki ma kira dreban naku ki sanar masa, ku da barin nan sai dare, zan mayar da ku da kaina." Murmushi kawai ta saki Maryama, sannan ta cigaba da latsar wayarta. Kiran Jiddah ne ya shigo mata, da hanzari ta ɗauka, saboda duk yinin yau take kiran Jiddah amma ba ta ɗauka ba. Har ma hankalinta ya soma tashi. Ga shi kuma tana son sanar da ita cewa ga ta a gidan su Aanur, coincidently ta zo, ashe wai yayan Dr. Islam Maman Abdul ce, kodayake dai ba ta santa da ita ba gaskiya. "Haba ƙawata miye duniya?" Maryama ta faɗa bayan ta ɗaga wayar. "Yi haƙuri ƙawata. Wallahi wayar ta shige cikin kujera tun safe nake neman inda ta shige ban sani ba. Sai fa yanzu Allah Ya sa aka gano min ita. Sorry ƙawata." Sai kuma ta ɓata rai, "Ai ni ma jiya da dare ina ta kiranki, missed calls ɗina nawa kika gani? Sannan kuma ba mun yi da ke Annur zai kira ki ba, amma kika yi kwanciyarki?" Dafe kanta ta yi ta ce, "Afwan Jiddalona. Akwai magana da dama a bakina. Amma bana gida yanzu, idan na koma zan kira ki ko zuwa dare." Jiddah ta ce, "Ni ɗin ma haka. Sai kin kira to." Ta tsinke wayar daga nan. 6:30pm A jigace ta shigo gidan, hankalinta tashe, idan ka kalle ta sai ka rantse cewa mahaukaciya ce. Mai gadi ne ya dakatar da ita, yana faɗin, "Ke ɗin wacece, kuma wurin wa kika zo?" Ajiyar zuciya kawai take saukewa haɗe da shessheka, ta gagara furta komai tsantsar tashin hankali. "Fice ki ba mutane wuri tunda ba za ki yi magana ba. Ana miki magana amma dan hauka sai wata shessheka kike? To tafi ki ba mu wuri ja'irar yarinya." Sai a sannan ta iya buɗe bakinta ta ce "Ba shi da lafiya, wallahi na gan shi da idanuwana." "Ni ban san wanda kike magana ba. Ki fito fili ki faɗi abin da yake tafe da ke. Idan kuma ƴar damfara ce ke sai in sani." "Wallahi ni ba ƴar damfara ba ce. Na ganshi Annur. Wallahi na ganshi a Maraɗi." Abdul da Muhammad da tuni suka isa falo domin kai rahoton wannan budurwar ne suka ci burki a bakin ƙofa. Muhammad mai wayon ya ce, "Yaya Maryama ga wata mahaukaciya can ta zo, sai faɗa mai gadi yake mata wai ta wuce ta ba mutane wuri. Ita kuma ta ƙi tafiya." Suna gama faɗin haka kuma suka ruga domin ci gaba da wasansu. "To fa! Mahaukaciya a gidan nan?" Momy ta furta cike da mamaki. "Gaskiya ba dai mahaukaciya ba. Amma dai Momy bara na je na gani." Islam ta faɗa haɗe da miƙewa. Maryama da Momy ma bin bayanta suka yi. Suna son su tabbatar da maganar Muhammad, kar a je ma shirme ne kawai irin nasu na yara. This page is in your honour, KHADEEJAH CANDY NOVEL GROUP. Kun ce wai last page ya maku kaɗan, to yau ga dogo nan na yi domin farin cikinku kawai. Fatan za ku ji daɗinsa fiye da wancan na baya. Kamar yanda na faɗa cewa fa akwai cakwakiya, to fa akwai ta ɗin. Ko kun hango ta kuwa? Shin Modu zai warke daga wannan babbar matsalar da take addabarsa? Asirin da aka ma Maryama zai yi tasiri kamar yanda su Annur suke muradi? Wane abu Hadiza za ta sanar ma iyayen Annur? Za su yarda da ita kuwa? Ta wace fuska Maryama za ta kalli lamarin? Duka wannan amsoshin suna a cikin labarin AMRAH NAKE SO! Kuma sannu a hankali duk za ku samu amsoshinsu. Fatan alkhairi ga masoyana baki ɗaya. Ku sani cewa ina ƙaunarku, ina yinku, iya wuya ana tare fi sabilillah. Thanks all. Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:51 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 3⃣8⃣ Follow me on wattpad: PrincessAmrah *** "Yauwa, gwara da Allah Ya jeho ku a daidai wannan lokacin." Ta faɗa tana mai sauke ajiyar zuciya, da yaƙinin tabbas mutanen uku da ke gabanta za su saurare ta, sannan kuma za su yarda da ita. "Baiwar Allah! lafiya? Me ke tafe da ke? Wurin wa ki ka zo?" Duka Momy ce ta fuskance ta haɗe da zaƙulo wannan kalaman daga ƙasan maƙoshinta, tana mai mamakin budurwar, ga ta dai da cikar zati, kyakkyawa bakin gwargwado, sai dai yanda kanta yake cike da kitson gashin doki, ga ta da hujen hanci har biyu, ko wane ta maƙala masa barima. A bisa goshinta an yi tsattsage an rubuta tafkekeiyar H. Laɓɓanta baƙi ƙirin, wanda da alama su ɗin ma caccake su ta yi. Fatar nan tata ta ji bleaching bakin gwargwado. "Uhm..." Ta faɗa tana mai haɗiyar yawu da ƙyar. Kallon da Momy ke watsa mata kaɗai ya isa ya karyar mata da guiwa, ta tabbata da ƙyar idan bayin Allah'n za su saurare ta. "Dama...uhm...ɗan ku, Annur ne, yana can Maraɗi yanzu haka na baro shi, ya haukace tuƙuru, sannan kuma zuciyarsa ba ta da lafiyar kirki, likita ma ya ce za ta iya bugawa a ko wane lokaci." Kallon mamaki suka watsa mata su duka ukun, ba su kaɗai ba, har mai gadin ma kallonta yake sake da baki. "Ku yarda da ni, wallahi da gaske nake maku. Ni da kaina ma zan kai ku har Maraɗi, har asibitin da yake kwance." Tana direwa nan ta share ƙwallarta, tana jiran sauraren martaninsu, shin za su yarda da ita? "Ina tababa a wannan bayanan naki. Na ma rasa gane inda suka dosa. Ko awanni shida ba a yi ba mun yi waya da Annur, kuma lafiya lau yake. Ban kuma san maganar da kike yi ba." Mamaki ya gama mamaye zuciyarta, ta ma rasa abin faɗi. Me ake nufi da ita kenan? Da gaske har awanni shida da suka shuɗe Annur lafiyarsa ƙalau? Ko dai ba su yarda da ita ba ne? Guje wa zargi ya sa Momy umurtar Islam cewa ta ɗauko mata wayarta a ɗaki. Babu ɓata lokaci kuwa ta nufi ɗakin, sai ga ta da wayar Momy a hannu ta miƙa mata. "Ba zan yi saurin gwasilarki, ko kuma ƙaryata ki ba. Dole sai na bincika, sannan in samu abin faɗi." Ta latsa lambar Annur, haɗe da kara wayar a kunnenta. Shiru Annur ba ɗauki wayar ba, har ta tsinke, Momy ta sake kiransa. Sau huɗu tana kiransa amma bai ɗauka ba, hakan ya fara karyar mata da zuciya, hankalinta ya fara tashi, ta fara tunanin gasgata baiwar Allah'r. "Ya salaam! Annur dan Allah pick my call. Kar ka bari zancen yarinyar nan ya zama gaskiya. Hauka? Ciwon zuciya? Kai a'a, wallahi ba dai Annur ɗina ba." Tana faɗin hakan tana sake kiran Annur amma shiru bai ɗauka ba. A karo na ba adadi da take kiransa ya ɗauka, a lokacin tana daf da tsinkewa, Bobby ya tashe sa daga barcin yamman da ya koma, ko salla bai yi ba. Da muryar barci ya ce, "Hello Momy." Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke. Ta dafe ƙirjinta da hannunta na hagu, tana jin yanda wani irin sanyi ke sauka a cikin zuciyarta. "Momy talk to me. Is there any problem?" "No...no, Annur. Kana ina ne?" Bayan ya sosa sumarsa ya ce, "Momy ina gidan su Farouk Sardauna. Tun 5pm da na tashi aiki sai na yo nan kawai, saboda na jima ban gaishe da Maminsa ba." "Ok, are you okay?" Ta sake tambayarsa cike da damuwa. "Am very okay Mom. Allah dai Ya sa lafiya." Murmushi ta ƙirƙiro ta ce, "Babu komai Annur. Please ka dawo gida mana, I need to see you, tun jiya rabon da na saka ka a idona." "Ok Mom. Zan dawo yanzu insha Allah." "Sai ka dawo." Tana gama faɗin haka ta tsinke wayar, tana bin Hadiza da kallo. Shiru ya biyo baya a tsakaninsu. Hadiza na mamaki sosai, saboda a hands free momy ta saka wayar, duk suna jin abin da yake faruwa. Sosai jikin Hadiza ke rawa, mamaki tsantsa a cikin zuciyarta. Ta ya hakan za ta faru? Wannan wane irin plan ne Annur yake yi? Me ya sa zai ma kansa ƙaryar ciwo? Idan kuma da gaske ne bai da lafiya, me ya sa zai ɓoye wa iyayensa? Ba ta samo amsoshin wannan tambayoyin ba ta ji Momy na faɗin, "Yarinya da alama dai ɓatar hanya kika yi. Ƙila kuma wani Annur ɗin ne daban, amma dai ba nawa ba. Tunda ga shi a gabanki mun yi waya lafiyarsa ƙalau. Idan ma wani makirci ne kika ƙulla, to haƙarki ba ta cimma ruwa ba. Idan kuma ke ƴar damfara ce, sai ki ƙara gaba, domin kuwa a nan dai ba ki yi nasara ba." Kuka sosai Hadiza ke yi. Ta ma rasa abin da za ta faɗa. Ba ta san me za ta ce su yarda da ita ba. Ita dai ta san shi ne ta gani. Tabbas Annur ne wannan marar lafiyar, domin kuwa ko Qur'ani za a ba ta ta rantse tsaf za ta rantse ɗin. Cikin muryar kuka ta ce, "Ku yarda da..." "Please get out from here. Mu ba sa'anninki ba ne da za ki tsaya kina neman yi mana wasa da hankali. Gwara ki taka da ƙafafuwanki ki bar gidan nan, tun ba a fitar da ke ba." Islam ce ta yi wannan maganar cike da masifa, ita dama in dai wurin tsiwa ne to tana gaba gaba, ta iya rashin mutunci sosai ba kaɗan ba. Shessheƙa take yi sosai, jikinta na rawa, kanta na sara mata, tana jin zuciyarta na mata zafi sosai da kalaman Islam. In dai masifa ce ita ɗin ma ta iya. Ta iya rashin mutuncin ita ma. Babu abin da Islam za ta gwada mata, domin kuwa ita ɗin kwarkwararriyar ƴar bariki ce. Ta zauna da wanda suka zarce Islam masifa, haka kuma ta san raddin mayar wa irinsu. Sai dai kuma a yanda zuciyarta ta yi rauni, take tsantsar tausayin halin da ta baro Annur a ciki, ko kaɗan ba ta jin za ta iya biye wa Islam su yi musayar kalamai. Ko ba komai ita ɗin ta haɗa jini da Annur, Annur ɗin da take ma soyayyar da ba ta taɓa yi wa wani ɗa namiji ita ba. A haka jiki saɓule ta miƙe, ta fuskanci Momy, da rawar murya ta ce, "Ku gafarce ni idan shigowar da na yi gidanku ta ɓata muku rai. Na muku alƙawari hakan ba za ta sake faruwa ba." Ta jawo haɓar gyalenta ta share hawaye. "In da a ce ko kaɗan kina da alamun kamala da zan iya ɗaukar maganarki. Sai dai kuma yanayinki kawai ya isa ya tabbatar da rashin ingancin duk wata kalma da za ta fito daga bakinki. Bara na baki shawara saboda gaba; duk inda za ki je ki yi irin wannan ƙaryar, to ki saka kayan mutunci. Wannan gashin dokin da kika sa ki tabbatar kin ɓoye shi. Ki ɗaura ɗankwalin da zai rufe miki goshinki. Hakan ne kawai zai iya saka wa a yarda da ke." Islam na gama faɗin haka ta kama hanyar barin wurin. Saboda kallonta ma kawai ƙara rura wutar tsanarta take a zuciyarta. A ganinta ba ta da babbar maƙiyya sama da Hadiza; ta nemi ɗaura masifu da bala'i ga yayanta. To miye amfanin tsayawa ta ci gaba da kallonta? "Malam Ya'u a tabbatar ta fita, sannan a kulle gida." Momy ta faɗa haɗe da bin bayan Islam, suka nufi falo. Maryama kawai aka bari tsaye wurin tana karantar Hadiza. Psycologist ce ita, ta yanayin mutum ma kawai za ta iya fahimtar wani abu game da shi. "Baiwar Allah zo ki fice cikin ruwan sanyi, tun ban ɗauko sandata ta shaɗi na zabga miki ita a gadon bayanki ba." Dakatar da shi Maryama ta yi da hannunta. Ta sake matsowa daf da Hadiza. Ta ce, "Zan iya yin magana da ke?" Ajiyar zuciya ta sauke Hadiza. Ta ji daɗi da Allah Ya sa mutum ɗaya na da hankalin da har ta nemi yin magana da ita. Kanta ta ɗaga alamar ehh. Ta ci gaba da kallon Maryama, tana tsananin mamakin irin kallon da take bin ta da shi. "Hajiya da kanta ta ce a kore ta. Dan haka ki yi haƙuri, duk wata magana da za ki yi da ita ba dai a nan ba, dan bana so na rasa aikina." "Damn it!" Maryama ta faɗa tana jin haushin mai gadin da ke magana iya gaskiyarsa. "Ba ni lambar wayarki, zan neme ki mu yi magana." Babu musu kuwa Hadiza ta fara karanto ma Maryama lambarta. Babu waya ma a hannunta, ta baro ta cikin gida. Sai dai a kanta ta haddace lambar. Bayan ta gama karanto mata ta maimaita har sau biyu, ta tabbatar daidai ne sannan ta bar wurin, Hadiza ma ta fita daga gidan. Ko da ta koma cikin falo ta tayar Momy da Islam na firar abin da ya faru. Mamakin wannan baiwar Allah'r kawai suke. Ko miye dalilinta na laƙaba wa Annur ɗinsu manya manyan ciwuka? Zama ta yi jiki babu ƙwari. Zuciyarta na karanto mata abubuwa da dama, wanda ta gagara sanin haƙiƙaninsu. Ƙoƙarin kawar da tunaninta take amma ta kasa, wuri ɗaya kawai ta tsurawa ido tun da ta zauna. Dr. Islam ce ta ce, "Da alama dai Maryama kina da raunanniyar zuciya. Yanzu ɗan abin da ya faru ne har yanayinki ya sauya?" Murmushi ta ƙirƙiro Maryama, ta ce, "Kawai dai na yi mamakinta ne. Haka kawai babu dalili sai ta zo ta kawo zancen ƙarya? Ba ta tunanin a lokacin da za ta zo ɗin Annur yana gida? Kuma wace riba za ta ci idan ta aikata hakan?" Cikin halin ko in kula Momy ta ce, "Ni fa na fi ganinta a ƴar damfara ce. Kun san yanzu da dabara suke aikin nasu. Ƙila kuma ƴar fashi da makami ce ta zo dan ta ga sirrin gidan." "Allah Ya fi ta kuwa. Babu abin da za ta iya yi mana wallahi." Islam ta faɗa cikin ɓacin rai. Daga haka har aka yi sallar magrib. Annur ya kira Momy cewa sai bayan ishai zai dawo, saboda zai yi meeting da wani company da suke son a ƙera masu ƙananan notina. Sosai hakan ya yi wa Maryama daɗi. Dama ba ta so ta haɗu da shi, ko dan kar ya santa ta dalilin Dr. Islam. Bayan sallar ishai suka ma Momy bankwana, Islam da kanta ta nufi kai su gida. A mota sai fira suke, tana nuna mata jin daɗin ziyarar da suka kawo musu. "Yanzu kuma sai yaushe, Muhammad?" Islam ta faɗa cikin fara'a. "Sai kuma gobe za mu dawo." Dariya suka saka daga Islam ɗin har Maryama. Dafe da baki Maryama ta ce, "Lallai ma Hammad a gaishe ka. Yo da wannan mu tsaya mu kwana mana." Caraf Muhammad ya ce, "Ai sai da na ce miki mu tsaya mu kwana kika ƙi. Gaskiya Maman Abdul mu koma, ban gaji da wasa da Abdul ba, ga shi kuma ya yi barci ko bankwana ba mu yi ba." "Allah Ya toni asirinki Maryama. Ashe dai kwana ɗan bawan Allah Ya so yi kika ƙeƙashe ko?" Dariya ta yi Maryama, ta ce, "Yanzu dan Allah Muhammad idan muka tsaya muka kwana, Mama fa? Duk yinin yau fa ba mu zaune tare ba. Good Friday guda amma ba mu gida." Baki tunzure ya ce, "Amma Yaya Maryama ba ga Easter Monday nan ba. Ai za mu zauna a gida mu huta." Ka yi haƙuri to. Yanzu dai mun riga da mun taho, sai kuma wani lokacin idan Allah Ya kai mu." "To." Kawai ya faɗa cikin kumburi, wanda har Islam sai da ta murmusa. "Aunty Islam ai za ki zo walimar saukar mu ko?" "Me zai hana? In dai kin tuna min idan lokacin ya zo, insha Allahu za mu zo, har Momy ma." "Zan kuwa tuna miki da yardar Allah. Ai an kusa ma. Ba zai wuce kwana goma ba. Amma dai idan ya rage kamar kwanaki uku zan kira na sanar da ke." A daidai isowarsu ƙofar gida Islam ta ce, "To Allah Ya nuna mana." Ta ce da Muhammad, "Hammad in ga hannunka." Miƙa mata hannun ya yi ta karɓa, kuɗi ta cusa masa a ciki haɗe da faɗin, "Kar ka buɗe har sai ka shiga gida. Ka gaishe min da Mama. Dare ya yi ai da na shigo mun gaisa." Bankwana suka yi cike da ƙaunar juna suka rabu. *** Tun daga lolacin da Hadiza ta bar gidan su Annur ba ta daina mamaki ba. Tana matuƙar son sanin ainahin abin da yake faruwa. Me Annur yake ɓoyewa ne haka? Ko dai wani ne wai ba shi ba? A zahirin gaskiya ita dai ta san Annur ne ta gani, ko tantama babu. Wane dalili ne zai sa ya zaɓi hauka a matsayin wani ƙulli na shi? Ta tabbatar kuma da shi ne Momy ta yi waya, saboda a handsfree ta saka, ta ji muryarsa. Dafe kanta ta yi a karo na barkatai, tana tunanin mafita. Latsa kiransa ta yi, cikin sa'a kuwa ya ɗauka a wanaan karon. "Babe..." Ya furta cikin sanyin murya. So take ta gwada shi, ta ga iya gudun ruwansa. Hakan ya sa ta ce, "My A...ina kewarka sosai. Lafiya dai ka daina ɗaukar kira na?" Da murmushi ya ce, "Ayyuka ne suka sha kaina da yawa. Amma yanzu komai ya daidaita. Kin dawo kenan?" A zuciyarsa kuwa dariya yake mata. Tunda ya ga ta kira sa da lambar Nigeria ya tabbatar cewa ta dawo, lokacin kwasar rabonsa ya yi. "My A ka san wani abu?" Ta faɗa cikin kakkausar muryarta, wadda ainahinta ba haka take ba, tsabar gwanancewa da bariki ne kawai ya komar da ita haka. "Sai kin faɗa babe." "Wani na gani mai kama da kai a Maraɗi, idan har ba mutum ya san ka sosai ba ba zai iya banbance ku ba. Ni kaina da ƙyar..." Dakatar da ita ya yi da faɗin, "Share kawai." Yana son ɓatar da zancen. Jin haka ya sa ta ƙara shiga wasi-wasi. Me ya sa daga fara magana zai dakatar da ita? Da alama ya san komai. Tabbas wani ƙullin ne, sai dai ita kanta ba ta san ainahin me yake nufi da hakan ba. Kawar da maganar ta yi ta hanyar jawo wani zancen na daban. Shi kuwa babban burinsa kawai su haɗu, domin ya kwashi abin da yake muradi. Suna cikin fira kiran Maryama ya ringa shigowa a wayarta. Duk da ba ta san lambar ba, haka kawai ta ji tana son datse wayar da Annur, domin ta ɗauki kiran lambar, wata ƙila kasuwa ce ta yi. * ** Na gaishe da Yayana Ibrahim Lawal Zaria. Ina matuƙar jin daɗin kulawarka a gare ni, da wanann littafin. Fatan kana isar da saƙon gaisuwa ta ga takwarata Amrah. Gaisuwa ta musamman ga Zulaihat Rano. Haƙiƙa ke ta daban ce, kin zarce su. Ina yin ki, ina ƙaunarki fi sabilillah. Rerbeeart_sk Zarah_bb ZulayheartRano89 khadeeja_Candy lamtana Kamala-Minna Soyayya fi sabilillah. Ban san ƙyashin da ke hana masu karatu danna alamar tauraron nan ba. danna shi na daɗa ƙarfafa min guiwa ta hanyar yi maku posting a kan lokaci. Yin biris haɗe da wuce shi kuwa harzuƙa zuciyata yake, in ji kamar na ringa ɗaukar tsawon mako guda ba tare da na yi posting ba 😂 RAZ 2 [8/30, 3:51 PM] Princess Amrah✍🏻💞: * 🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 3⃣9⃣ Wattpad me @ PrincessAmrah *** Sallama ta yi mata Maryama. Muryarta sanyaye, tana mai jin daɗin ɗaukar kiranta da Hadiza ta yi, dan a tunaninta ma ko ba daidai ta hardace lambar ba. Amsa sallamar ta yi Hadiza. Tana son gasgata muryar, saboda tun ɗazu take tsumayen kiran Maryama. "Fatan kina lafiya. Sunana Maryama..." Ba ta ƙarisa maganar ba Hadiza ta tare ta da, "Wadda muka haɗu gidan su Annur?" "Exactly." Maryama ta furta a hankali. Gaisawa suka yi sama sama, kafin Maryama ta ce, "Ina son sanin haƙiƙanin abin da kika faɗa ɗazu ne. Dan Allah ba na so ki min ƙarya. Ki faɗa min iya gaskiyar abin da kika sani. Please!" Ta ƙarashe maganar da muryar magiya. "Ban san taƙamaimai me zan faɗa miki ba Maryam. Ni kaina a rikice nake, baki ɗaya kaina ya ƙulle. Da gaske nake, wallahi da gaske nake na ga Annur a Maraɗi. Amma abin da ya rikitar da ni, yanzu haka na yi waya da Annur, alamun lafiyarsa ƙalau, kuma na fara masa maganar na ga mai kama da shi, ya nemi shashantar da maganar." Dafe kanta ta yi Maryama. Cikin tausasshen lafazi ta fara ajje kalamanta, tana mai tsananin son Hadiza ta fahimce ta, tare da ba ta iyakar amsar da ta sani. "Hadiza...please ya kike da Annur? Ke ɗin wacece? Ƴar wane gari ce? Me ya kai ki Maraɗu da har kika ga no mai kama da Annur?" A daburce ta ce, "Ba mai kama da shi na gani ba, wallahi shi na gani. Ko za a yanka ni ba zan daina faɗar Annur na gani ba." Ajiyar zuciya ta sauke Maryama, ta ce, "Na ji, na yarda Annur ne kika gani ba mai kama da shi ba. Ki ba ni sauran amsoshin tambayar da na miki." Ko kaɗan ba ta son zancen. Abun kunya ne gare ta ta iya buɗar bakinta ta ce ita karuwa ba ce. Karuwar Annur, wacce ta gudo daga garinsu kawai saboda zaman kanta. "Are you with me?" Maryama ta tambayi Hadiza, jin ta yi shiru, kuma tana jin saukar numfashinta, alamun dai tana saurarenta kenan. "Uhm...na san shi ne...yana so na." "Dadiron ki ne?" Ta tsinkayo muryar Maryama ta mata wannan tambayar, cikin halin ko in kula. Tunda take ba ta taɓa jin haushin kasancewarta wacce za a iya ambato da wannan kalmar ba sai yau. Me ya sa ba ta zama wacce za ta iya bayyana ko ita wacece ba a duk inda za ta tsinci kanta? Me ya sa take rayuwar da ita kanta take jin kunyar bayyanar da kanta a irin rayuwar gaban wasu mutanen? Haka kawai take jin ƙwarjinin Maryama. Ta rasa dalilin da ya sa take ganin darajarta, sam! Ba ta jin za ta iya yi mata ƙarya. Kuma a dukkanin yanayin Maryama idan aka mata ƙarya sai ta gane. Da ƙyar ta iya bultso magana daga bakinta. Laɓɓanta na lugude ta ce, "Ehh...abokina ne, yana biya min buƙatata, ni ma kuma ina biya masa ta sa. Ni ƴar Nijar ce, karuwanci ya gudo da ni daga ƙasarmu. Maraɗi ne garimmu, can ne asalina. Na je wurin wani biki ne na dangimmu, har Allah Ya sa na ga Annur ɗin a can." "Biki...?" Maryama ta ambata tana mai ci gaba da, "Bayan kin gudo kin kama zaman kan ki ne kuma har kika iya komawa wurin wani biki? Kenan hakan ba zai iya zama wani abu ba a gare ki?" "Tabbas! Hakan ba komai ba ne." "Anyways, lets back to our business. To ke yanzu ta wace fuska kika kalli abun? A tunaninki tabbas Annur ne kika gani? Idan shi ne, me kike tunanin ya sa ya aikata hakan?" "Abin da na kasa ganowa kenan. Zuciyata ta kasa tantance min gaskiyar wannan lamarin. Na kasa fitar da abun daga zuciyata. Wallahi a yanayin da na samu Annur abin a tausaya masa ne, abun ya zauna a zuciyarka ne." "Shi kenan to. Yanzu idan na nemi taimako daga gare ki, za ki iya taimaka min?" "Me zai hana?" Hadiza ta gaggauta tambayar Maryama. "Yauwa to. Ba zan so na zo inda kike ba gaskiya, saboda hakan zai iya zubar da kima ta a idon jama'a, ba za a iya gane dalilina na zuwan ba. Ya kenan?" Shiru ta yi Hadiza tana nazari, dan ba ta san amsar da za ta ba ma Maryama ba. "Uuhm..." Maryama ta ambata. "Ya kike so a yi?" "Ko za mu yi mahaɗa?" "Idan hakan kike so ya yi. Sai ki faɗa min inda za mu haɗu ɗin ina jira." Za ta kashe kenan Maryama ta ce, "Wait, a minute please...dan Allah kar ki sanar ma kowa wannan maganar. Ina so ta zama sirri a tsakanimmu, ko Annur ɗin kar ki faɗa ma wa." "Ba zan faɗa ma kowa ba na miki alƙawari." Bankwana suka yi daga nan suka kashe wayoyinsu. Latsa kiran Jiddah ta yi Maryama. Babu ɓata lokaci kuwa Jiddah ta ɗauka. Bayan sun gaisa ne ta kwashe komai ta sanar da Jiddah, har wayar da suka yi da Hadiza yanzu. "Am totally confused. Baki ɗaya kaina ya ƙulle, na kasa hango komai Jiddah. What can you say? Please hint me, little, Jiddah!" Kanta ta gyaɗa kamar tana gaban Maryama ne, ta ce, "Akwai ɗaure kai sosai lamarin. Me ye zai kai Annur Maraɗi cikin awoyin da ba su wuce shida ba? Me zai sa ya ga Hadiza a Maraɗi, kuma ya ƙi nuna ya santa, bayan kuma dadironsa ce? A tunanina ko kaɗan ba zai ɓoye mata kanshi ba, saboda ya san ta san komai game da shi. Ta gama sanin sirrinshi tunda har ya kasance ma'aboci aikata zina da ita." Shiru Maryama ta yi na tsawon lokaci, kafin ta iya zaƙulo magana daga bakinta, ta ce, "Ko kaɗan tunanina bai ba ni cewa Annur ne ta gani ba. Saboda a yanda ta siffanta shi, babu yanda za a yi cikin ƙanƙanin lokaci ya yi wanann ɓadda-kamar. Kuma ma idan ɓadda-kama zai yi, sai in ga ai a nan Nigeria zai yi ta. Ban ga dalilin da zai sa ya tafi Nijar ba." Murmushin takaici ta yi Jiddah, ta ce, "Ba abun mamaki ba ne dan ta ce shi ne a Maraɗi. Ai kin ga Annur ya taɓa samun taɓin ƙwakwalwa, kuma wanda ya samu matsalar hauka, a kowane lokaci ya kan iya tasar masa. Ta yiu ya taso masa ɗin ne bayan ya je can, tunda mutum kamar Annur dama ba za a raba shi da shiga cikin Nijar ba." "Jiddah na fara tunanin wani abu. Na yarda da kalaman Hadiza ɗari bisa ɗari. Na fara zargin ƙila dai mai kama da shi ne ta gani. Kin san fa akwai irin haka." "Haka ne tabbas. Amma yanzu ga shawara ɗaya." "Ina jin ki Jiddah...Allah Ya sa mai ɓullewa ce." Jiddah ta ce, "Kawai ki ma Bobby maganar kai tsaye cewa Annur ya ce yana son ki. Tunda yana yawaita faɗar zai iya ja da duk wanda ya nemi raba ki da shi, a ganina zai iya tona asirin Annur, in ma da wata ƙullalliya da yake ƙullawa ne" "Good idea." Maryama ta furta cikin murya mai nunar da ta ji daɗi. Bankwana suka yi da juna, Maryama ta kashe wayar, tana jin sassauci a cikin zuciyarta. *** Daga gefensa take zaune, butsu butsu ta ɗaga kanta ta dube shi, cikin tausayi da ƙara jin soyayyarsa a cikin zuciyarta. "Amrah..." Ya furta a cikin baccinsa wahaltacce da Dr. Huzaif ya narka masa allurar barci sannan ya samu ya yi. A hanzarce ta miƙe tsaye tare da isa dab da gadon. Tsura masa idanuwa ta yi, kyam ta ke kallon fuskarsa. Kyakkyawa ne sosai. Hancinsa a tsaye yake siriri, bakinsa ɗan ƙarami wanda ya gama farfashewa, duk ya bi ya lalace tsabar wahala. Gyaɗa kanta ta yi ta gaggauta dawowa a cikin hayyacinta. Tunanin banza take a ganinta, tunda dai ga shi a kwance yana fama da kansa, me zai sa ita ta zurfafa a begensa? "Amrah...Amrah nake so!" Ta sake jin Modu ya ambata duk a cikin barcinsa da yake yi na wahala. "Modu nice ag gabanka hwa. Buɗe idanuwanka ka gani Fiddou ce hwa ba Amrah ba." Bai ma san tana yi ba, sai a hankali ta jawo abin rufa ta rufe shi cike da tausayi, ta kama hanyar komawa zamanta za ta zauna. Jin sallamarsa ta yi ya shigo, hannunshi da leda babba, ya ƙarisa shigowa cikin ɗakin. Da fara'arta ta amsa masa sallama, ta fasa zaman har sai da ya iso inda take. "Sannu Fiddou! Ya giɗe yaƙ ƙara ji da jiki?" "Da sauƙi dai." Ta furta haɗe da gyaɗa kanta, hawaye na neman fara kwaranya daga idanuwanta. "Ya isa giɗe ba kuka nat tambaye ki ba. Insha Allahu yana samun lahiya ba da jimawag ga ba. Kuma na tabbata likita zai ba shi kula yanda yak kamata. Ki kwantar da hankalinki." Shiru ta yi da kukan, sai dai kuma hawaye bai daina fita ba. Tausayinsa take ji. Ko kaɗan ba za ta taɓa iya jurewa ba, ba za ta iya yarda da maganar Dr. Huzaif ba. "Mahmouda ba na tunanin Modu zai warke. Likita da kai nai yac ce giɗe ga shi yana cikin yanayin matsala. Ka gan shi nan hwa barcin wahala ne yake. Ciwo yad dame shi, likita yai yi mai allurar barci. Yanzu kana ganin wanda zai warkewa ne ba zai taɓa samun sauƙi ba sai idan yana barci?" Shiru ya yi Mahmouda. Ko kaɗan ba ya son ya ƙara tasar mata da hankali ne. Amma fa ko shi ba ya ba Modu tashi. Babbar matsalar da abin ya shafi zuciya; yana da wuya wanda zuciyarsa ta samu matsala ya tashi, sai dai idan dama ba daga zuciyar ba ne, saboda wasu matsalan ƙirji ne kawai suke fama da shi sai su ce zuciyarsu na ciwo, alhali in zuciya ce ma ba za su faɗa ba, sai dai a gane. A tsayen da suke suka fara ganin Modu na motsawa, yana ƙoƙarin buɗe idanuwansa da suka gama kumbura tsabar kuka. Da hanzarinta ta isa gare shi tana ambaton sunanshi, "Modu..." Ta zauna a bakin gadon haɗe da taimaka masa wurin tashi. "Sannu Modu. Yanzu kam nan ɗin ka ya bar ciwo ko?" Ta gwada masa saitin da tata zuciyar take. Baki kawai ya washe mata yana bin ta da kallo. Murmushi ta sakar masa sannan ta miƙe tsaye. "Nurse ta ce idan kat tashi in hwaɗi mata. Za a yi maka gwajin zuciya. (Electrocardiogram (ECG) )" Barin ɗakin kawai ta yi, ta nufi nurses station. Bayan ta sanar da nurse ɗin ne ita kuma ta samu likita ta faɗa masa. Izini ya bayar cewa ta je da wasu daga cikin nurses maza, a je da Modu electrocardiograph room (ɗakin da injin ɗin yin ECG yake) don yi masa aikin yanzu. Hakan ce kuwa ta kasance. Sai da suka haɗa da dabara kafin Modu ya yarda ya ɓaɓɓako daga bisa gadon, jin sun ambaci sunan Amrah; da duk iya taurin kansa in dai aka ambaci wannan suna, to fa tabbas zai aikata duk abin da aka umurce sa. A bisa ƙafafuwansa yake taku, akasin tunaninsu kenan. Su a tsammaninsu ma ba zai iya yin tafiyar da kanshi ba, dalilin ma da ya sa likitan ya haɗa da maza kenan. Amma da mamakinsu, ambatan sunan wata mace ya saka shi dauriya haɗe da yin tafiya da kansa. ECG room ɗin suka nufa kai tsaye, a buɗe suka tarar da shi, Technician ɗin da zai masa gwajin suka samu har ya shiga ciki, su kawai yake jira. A bisa gado suka kwantar da shi, nan take ya fara ƙoƙarin yi masa gwajin, da na'urar yin aikin. Bai fi minti biyar zuwa goma ba ya kammala, saboda dama ba wani ɗaukar lokaci ake wurin yi ba. Bayan an gama ya je ya ma likitan magana cewa ya kammala, sai ga shi kuwa har room ɗin ya zo ya zauna a bisa kujera, Technician ɗin kuma ya fita ya bar shi da result ɗin a hannu. Shi kanshi ya yi mamakin result ɗin na Modu; yanda ya tsammani ciwon kwata-kwata ba haka yake ba. Ashe ma bai wani ta'azzara sosai ba. Abin da ya sa Modu ɗin yake yawan jin ciwon, saboda abin ya shafi zuciya ne, ita zuciya kau ko kaɗan ba ta son baƙon abu, duk yanda wani abu ya nemi kawo mata tangarɗa, fat ɗaya za ta iya aika mutum lahira. Hamdala ya yi bayan ya zauna. Kwance yake Modu idanuwansa a rufe, Dr. Huzaif na bin sa da kallo. Riyawa yake a ransa akwai magunguna manya guda biyu, wanda ya tabbata ko su kaɗai sun isa su kawo waraka ga zuciyar Modu. Bayan haka kuma, zai ƙoƙarta kyautatawa haɗe da faranta masa, zai barsa da zama a asibitin na wani lokaci ba tare da ya ba shi sallama ba, dan ya samu kula mai kyau. Dan da ganinshi an san ba wani galihu ne da shi ba, ita kanta Fiddou ɗin ba lokacin kula da kanta sosai gare ta ba, to bare kuma Modu mai larurin da dole sai an yi taka-tsan-tsan. Jijiyoyin da suke aika jini zuwa zuciyar Modu ne suka ɗan samu tangarɗa, sai kuma wadda ke kai jini har ciki kidneys ɗinsa. Kuma duk fargabar ko kuma damuwar wani abu ce ta haddasa hakan. PA ɗinsa ya ƙwala ma kira ya zo, ya aike shi ya kira masa Fiddou. Babu jimawa sai ga ta ta zo, hankalinta a tashe, fargabar abin da za ta ji daga bakin likitan kawai take. Wurin zama ta nema bayan ta yi sallama ya amsa, ta tsurawa inda Modu yake idanuwa, tana kallon yanda ko motsi ba ya yi. "Uhm..." Ta jiyo shi ya yi gyaran murya, alamun yana da buƙatar karkatowar hankalinta gare shi. "Duk yanda na tsammani ciwon ba haka yake ba. Yau kam za ki ji hwarin labari daga gare ni." Ya faɗa haɗe da kanne mata ido ɗaya. Duk da ta ji daɗi sosai a zuciyarta amma ba ta bayyana masa ya gane ba, saboda haushinsa da take ji. Nannauyar ajiyar zuciyar da ta sauke kuwa ita ta tabbatar masa da cewa ta matuƙar jin daɗin furucinsa. "A cikin kashi ɗari na zuciyar Modu, kashi talatin da biyar za a iya cewa ya gurɓata, ma'ana shi ne yake masa ciwo. Kashi sittin da biyar na zuciyarsa lafiya lau take. Wannan kashi talatin da biyar ɗin ne yake damunsa, shi ne yag gagara daidaita tafiyar numfashinsa, da kuma bugun zuciyarsa yanda ya kamata. Magunguna ne zan rubuta mai, wanda nake da yaƙini da amincewar Allah in dai ya yi anhwani da su tabbas zai samu waraka, zuciya tai za ta koma aiki yanda aka son ta yi." Ya dakata daga nan, ya ɗan juyar da kallonshi zuwa ga Modu, sannan ya sake kallonta ya ce, "Matsala guda ɗai ce..." "Da ma na sani walle. Dole dai sai ka tayar min da hankali. Wai dan Allah kai wane irin likita kake?" Murmushi ya yi wanda har sai da fararen haƙoransa suka bayyana. Ya ɗan tauni leɓonsa na ƙasa, ya lumshe idanuwansa duka biyun, sannan ya buɗe su a fuskar Fiddou. Duƙar da kanta ta yi ƙasa, tana mai jin takaicin ha ido da shi, saboda muguwar tsanar da ta masa. "...matsalar ita ce, magungunan suna da tsada sosai, dole sai an fitar da maƙudan kuɗi wurin siyansu." Dafe gabanta ta yi da jin kalamansa. Lallai kuwa matsala mai girma. Ita yanzu ya za ta yi ta samu kuɗin siyan wannan magungunan? Ta kanta take. "Duk kati guda yana kai sefa dubu ɗaya da ɗari biyar, kuma sai ya sha a ƙalla kati huɗu. Gudan shi ne ad da sauƙin kuɗi; yana kai saifa ɗari takwas, kuma shi kati guda ne zai sha. Insha Allahu matuƙar ya sha wannan magungunan a kan tsari, giɗe zai samu lahiya, matsalar zuciya kuwa sai dai wata ta taso, ba dai wadda yake kan yi yanzu ba." Sosai da ji daɗin maganarsa ta ƙarshe. Har da murmushin farin ciki ta saki. Sai dai kuma ba a nan gizo yake saƙa ba, a ina za ta samu wannan maƙudan kuɗin wanda za ta siya ma Modu magani? Ta dafe kanta, zuciyarta na jefa ta wata duniyar ta daban, ba tare da ta san ta isa ba. "Jinkirin siyansu kuwa, tabbas zai iya dagula komai, ciwon na shi ya kai inda ba za a ji daɗi ba. A yanzu haka bugun zuciyar Modu a hankali a hankali yake tafiya, saboda wanann jijiyoyin da ba su aika jini yanda ya kamata (blood vessels). Wannan matsalar da kike ga kamar ƴar kaɗan, tsaf za ta iya dagula komai. Kin ga a yanzu haka yana fama da matsalan ciwon ƙirji, wanda duk waccan matsalar ce sila. Sannan kuma numfashinsa ba ya tafiya yanda ya kamata. Irin wannan matsalar takan haddasa yawan ƙunci, da mutum ya ringa tunanin ya kusa mutuwa, dan ma dai shi ɗin ba hankalinsa ɗaya ba. Tana saka yawan gajiya; ki ji ko ba abun gajiya kika yi kina yawaita gajiya, komin ƙanƙantar abu. Za ta iya saka wa ki ringa jin nauyi sosai a ƙirjinki, kamar an ɗaura miki wani nannauyan abu, wanda ba za ki iya sauke shi ba." Ya ɗan dakata daga nan, sannan ya ci gaba, "Dole zai daina cin duk wani abu wanda ya shafi cholesterol (masƙi) na tsawon wani lokaci, har mu ga yanda Allah zai yi da shi. Akwai wani mai na nan na musamman non cholesterol ne, ko abinci zai ci da shi ya kamata a yi amfani wurin girkawa. Kar ya sha madara, gyaɗa, mangyaɗa, manja, nono da sauransu, duka dai zan rubuta miki a takarda idan na koma Office. Magungunan da za a nema shi DIXOGIN yana taimakawa ne wurin aika jini, ya isa cikin gaggawa, kamar yanda ya kamata ya tafi, zai improving blood circulation. Shi kuma DIURETICS yana taimaka ma magudanyar zuciya zuwa ƙoda ne, ya taimaki ƙoda wurin tace gishiri da kuma suga wanda ba a buƙata, it makes it easier for your heart to pump. These medicines are very important." Ya yi shiru daga nan, yana karantar yanayinta mai cike da tsantsar tashin hankali mara misaltuwa. Kallonsa kawai take, ba ta san sanda hawaye suka fara wanke mata kumatu ba. Bayanan nasa ma jinsu kawai take, ba wai komai ne take fahimta ba, musamman ma da yake faɗo mata kalmomin da tunda take a rayuwarta ba ta taɓa jin su ba. Ita daga Hausarsu sai French wanda ba za a rasa ba kawai take ji. Shi kuwa dama a US ya yi karatunshi, ba zai taɓa iya magana ba dole sai ya sirka turancin, saboda ba komai ne zai ce ya sani da French ko kuma Hausa ba. *** Ku ma page ɗin nan kyakkyawar fahimta, wata ƙila zai ma da dama daga cikin masu karatu amfani nan gaba. Na gode, na gode, na gode ƙwarai masoyana. Har ma ban san da bakin da zan gode muku ba. Ina yin ku, ina son ku, ina ƙaunar ku fi sabilillah. To Gosties👿 kun san kanku, ehen...kuna discouraging ɗina. Shin aikin wahala ne dan ka danna wannan ƴar tauraruwar kawai don ka faranta min rai? Ina tsananin jin daɗin in ga an yi voting, sai in ji ƙarfin guiwar yin typing kodayaushe😁 Duk wacce ke son na yi posting gobe ta ɗaga hannunta. Idan na ga yawanku zan maku, idan kuma na ga babu votes, alamun dai ba kwa son post gobe ne.😎 Me kuke hasashe? Shin yaya Fiddou za ta yi da wannan bawan Allah, wanda yake da buƙatar taimako a halin yanzu? A ina za ta samu kuɗin siya masa wannan magungunan? Ɓangaren su Maryama kuwa, ko kuna hangen nasara a tattare da lamarinsu? Idan sun yi wancan plan ɗin ya ɓaci, shin kuna tsammanin za su dace a wannan? Drop your comments, and then forward it to family and friends🙌 PINKY DURLING RAZ 2 [8/30, 3:52 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 4⃣0⃣ Follow me on wattpad: PrincessAmrah *** Tashi ta yi jiki babu ƙwari, hawaye bai daina kwaranya daga idanuwanta ba, tunani fal a cikin zuciyarta. A hankali take taku har ta isa ɗakin Annur, wanda ta baro Mahmouda a cikinsa. Ganin yanayinta da ya yi kawai ya tabbatar masa cewa ba lafiya ba. Kuka take wiwi, har da shessheƙa sosai, hannuwanta duka biyu a ka. A rikice ya miƙe tsaye, ya fara gyaɗa kansa, cike da tausayi ya ce, "Ki bar kuka giɗe, Allah'n da Ya halicce shi ya hi mu so nai, idan kuma ya tahi ne, to tabbas lokaci nai ne ya yi. Ina gudun kar a yi biyu, ke ma ki kamu da wani ciwon." Rijif! Ta faɗa ƙasa da ƙarfi ta zauna. Kanta ta haɗe da guiwowinta, tana ƙoƙarin shanye kukanta. "Ya jiki nai? Halan dai da rai nai? An ƙare wancan awo?" Duk a jere ya sako mata wannan tambayoyin. Da ƙyar ta samu ta ɗago kanta, cikin sanyin murya ta ce, "An ƙare wancan awo yana can yana barci, saboda waccan allura ta barci da aka yi mishi ba ta ƙare saki nai ba." Da mamaki ya ce, "Ah, to mi da kike kuka halan?" Haɗiye sabon hawayenta ta yi, ta ce, "Likita ya hwaɗi min magungunan da za a sai ma Modu, wanda siyan su ɗai ne zai sa Modu ya samu sauƙi. Suna da tsada sosai, ko ni ban san inda zan samu kuɗin siyan su ba." Gyaɗa kansa ya yi, da tausayi ya ce, "Halan har nawa ne kuɗin?" Bayani ta masa na kuɗin maganin, da kuma adadin wanda ake so ya shanye. Ta ƙarashe da faɗin, "Ya ce duk da abun ba mai girma sosai ne ba, zai iya zama mai girma in dai ba a daure an sai mai maganin nan ba." Da sabon kuka ta dire maganar, ta sake duƙar da kanta a guiwowinta. Dafe kansa ya yi, zuciyarsa na masa raɗaɗi, tausayin Modu yake, ji yake tamkar ciwon a jikinsa yake. Ina ma dai a ce yana da kuɗin siyan maganin nan? Bai da su. Shi kan shi rufin asiri ne da shi. Lokacin da ya kaɗe Modu ma daga wurin neman aiki ya dawo, kuma bai samu ba. Tashin hankalin da yake ciki a lokacin, ba wai na lururar mahaifiyarsa ne kawai ba, har da takaicin wahalar da ya sha wurin neman aikin, kuma a ƙarshe ya ƙi samu. Ajiyar zuciya ya sauke, cikin kwantar da hankali ya ce ma Fiddou, "To do Allah dai ki cire damuwag ga daga cikin zuciyarki. Kar wani abu ya same ta, kin ga dai yanda ta Modu tai yi." "Ba zan iya ba, ba zan iya ba Mahmouda! Modu na cikin haɗari, haɗari mai wuyar shawo kai. Ban san yanda zan yi ba, ba ni da halin taimakonsa." "Allah zai rufa asiri, ki kai kokenki kawai wurinSa, ba Ya gyangyaɗi Allah, Yana jin ƙan bayinSa, Yana kuma karɓar adduar bayinSa a duk sanda suka kai maSa kokensu." Shiru kawai ta yi tana kallonsa. Mamakinsa take, mamakin kalamansa take. Ta ya za ta iya kwantar da hankalinta bayan kuma ba ta da wata mafita? *** Mai napep ɗin take ɗaga ma murya ta yanda zai iya jin ta sosai, saboda sautin da ya kunna a ciki. "Mallam!" Ta faɗa a karo na biyar, da ƙarfi fiye da yanda ta kira shi a baya. Rage sautin ya yi sannan ya ce, "Lafiya? Ai kaman ba a zo inda zan kai kin ba." "Ehh ga shi tana kira na cewa mu dakata ta hange ni. Dama ita ce ba ta yi kwatancen da kyau ba." Reverse ya yi, saboda sun wuce ta da yawa. Bayan sun kai inda take ta sauka, ta miƙa masa kuɗinsa sannan ta ta yi taku uku, wanda ya kai ta gaban Hadiza. Hannu ta ba ta suka gaisa. Da fara'a Maryama ta ce, "Ai da mun zarce kuwa." Ita ma Hadiza ta yi murmushin, ta ce, "Ban wani san kan area'n sosai ba, shi ya sa ma na zaɓi nan ɗin. Kuma ga shi babu hayaniya sosai, babu ƴan sa ido." "Haka ne." Hadiza ta faɗa. "Mu je. Akwai wani babban lambu ta can baya. Sai mu biya kuɗin shiga mu shiga, kamar za mu fi samun natsuwa a ciki." Bin bayanta ta yi suka nufi hanyar lambun, ba su wani yi tafiya mai nisa ba suka isa. Maryama ta fiddo kuɗin za ta bayar amma Hadiza ta hana, ita da kanta ta ciro kuɗin ta bayar. A bisa wasu ƙayatattun kujeru suka zauna, babu jimawa aka kawo musu lemuka aka jera a gabansu. Ajiyar zuciya Maryama ta sauke, ta ce, "Mun fara magana a waya." Buɗe robar fanta ta yi Hadiza, ta ɗan kurɓi kaɗan, sannan ta rufe, ta ajje a gabanta. Fuskantar Maryama ta yi da dukkan nutsuwarta, ta saita idanuwanta a cikin nata, ta ce, "Yanda duk na faɗa miki a waya to hakan ne. Annur ko kaɗan bai zama mutumin kirki ba, face fasiƙi! Mazinaci! Mayaudari!" Ta yi shiru daga nan, sannan cikin rauni ta ci gaba, "Ina ƙaunar Annur, da dukkan zuciyata. Ina burin ya kasance nawa, na har abada. A da, ban taɓa tsammanin akwai namijin da zan ma soyayyar tsakani da Allah ba. Ban taɓa tunanin zan so yin aure a wannan ɗan taƙin ba. Sai ga shi na dulmiya, ban farga ba, zuciyata ta tsunduma da ƙaunar Annur Iqra Al-hussein. Ƙaunar da nake masa ta gaskiya ce, wacce hankalina zai tugunzuma a duk sanda zan ganshi cikin wata larura, ko kuma damuwa. Wannan dalilin ne ya sa zuciyata ta ba ni tabbacin Annur ne na gani a Maraɗi. Zuciyata da ta shi kamar akwai wani connection a tsakaninsu; wanda ke ba ni tabbacin cikin halin da rayuwarsa take. Abin da na kasa in gane shi ne, shin a cikin awanni shidda ne Annur ya tafi Maraɗi? Me ya kai shi? Me zai shigar da shi cikin wannan halin, ba tare da iyayensa sun sani ba? Akwai alamar tambaya a zancen nan. Da alama dai akwai ɓoyayyen al'amari, wanda daga Annur ɗin sai mahaliccinsa kawai suka sani..." "Sai kuma abokinsa Farouk Sardauna!" Ta tsinkayo muryar Maryama ta faɗa, tana jinjina kai. "Na tabbata Bobby bai rasa masaniya dangane da wannan al'amarin, tunda kansu a haɗe yake, gudansu ba ya yin abu ba tare da shawarar guda ba. Duk wani mugun halinsu tare suke aikata shi." Ta dakata daga nan, jin wayarta na ringing. Dubawa ta yi sai ga sunan Bobby ɓaro ɓaro ya fito, hakan ya sa ta sakin murmushi, ta ce, "Kin ga ɗan halak!" Ta amsa kiran, tana ƙoƙarin gyara muryarta daga ta murmushin da take, zuwa ta asalin Maryama ɗinta. "Hello-salamu alaikum." Ta furta a tsanake, da muryarta dallah-dallah. "Maryama ya kike? I have been calling you amma bakya ɗauka. Fatan dai kina lafiya. Ya gida? Ya school? Wai, ashe hutun easter ake. Ya su Mama? Ya..." Ta gaggauta dakatar da shi, dan wannan surutun na shi ba mai tsayawa ba ne. "Everything is okay." Ta faɗa a takaice, tana kuma jiran abin da zai faɗa. "Uhm...dama Maryama please ina so ki ba ni lokaci mu haɗu. Ina da buƙatar ganinki, idanuwana na matuƙar son su yi tozali da kyakkyawar fuskarki, mai cike da walwala." 'Ya Allah!' Ta faɗa cikin zuciyarta. Surutun Farouk yawa ne da shi. Duk haƙurin mutum sai ya ƙule sa. "Farouk na sha faɗa maka cewa iyayena ba za su taɓa bari na tsayuwa da kai ba. Na rasa me ya sa ba ka fahimta. Ba wai ba na sonka ba ne, wallahi halayenka ne ba na ƙauna. Kai ma ka san ba ka da wani abu da zai sa a ƙi ka, fa ce gurɓatattun halayenka, wanda babu na ɗauka a cikinsu." "Da sauƙi Maryama. Tunda dai kina so na shi kenan, kin gama min komai wallahi. Na tabbata iyayenki abin da kike so shi za su so. Wallahi zan zama na kirki saboda ke..." "Saboda ni?" Ta tari zancen nasa. "Kenan ba saboda Allah za ka nadama ba? Ashe dai tubar ba ta zama ta kirki ba kenan. Duk abin da aka yi saboda wanin Allah, to wannan abun ya zama riya, Farouk." "Please ki fahimce ni, ba wai ina nufin haka ba ne." "Ya kake nufi Farouk? Hausa fa ka yi, wacce kai tsaye za a iya fahimtarta." "Yanzu dai ba wannan ba. Ki min alƙawari in dai na daina komai za ki aure ni." Ya marairaice murya haɗe da yin wannan maganar. "Ni kam ba wannan ba, akwai maganar da nake so mu yi da kai." Ajiyar zuciya ya sauke haɗe da faɗin, "Allah sa alkhairi ne." Bayyanannen murmushi ta yi, irin mai narkar da zuciya ɗin nan, wanda ke faranta ran Farouk Sardauna. "Alkhairi ne ma." Ta ɗan dakata haɗe da murmusawa, sannan ta ce, "Wai dan Allah waye Annur?" Shiru ya ɗan yi na tsawon sakan goma, kafin ya ce, "Wani abu ne?" Ya gaggauta tambayarta. "No, kar ka zata wani babban abu ne. Kawai dai tambayarka na yi." "He's my best friend. A best friend of mine." "Good. Can you tell me little about him?" "Yes, why not?" "Great." Ta faɗa haɗe da gyara zamanta, ta ɗan kalli fuskar Hadiza da murmushi. Ita ma Hadiza murmushin ta sakar mata, duk da yake ba ta san inda zancen ya dosa ba. "He's Annur, a son of Pharm Iqra Al-hussein. He's a nice person. Mutumin kirki ne mai riƙon addini..." "Kamar kai kenan?" Ta tari zancensa tana murmushi. Shiru ya ɗan yi kafin ya ce, "What do you mean?" "Just a question." Ta ambata har yanzu ba ta daina murmushi ba. Ko kaɗan ba ya jin zai iya kasa faɗawa Maryama tambayar da ta masa. Amma wallahi in da a ce wata ce ba ita ba, har marinta yana iya yi idan ta masa wannan tambayar banzar. Idan kuwa a waya ne to tsaf zai iya zagin iyayenta, sannan a ƙarshe ya kashe kiran. "Lemmi tell you the fact; Annur is a nice person, as I told you. But...ehm...duk halayemmu iri ɗaya ne. Amma dan Allah me ya sa kika min wannan tambayar?" "Babu komai fa. Kawai dai ƙawata yake so ne, shi ne take faɗa min sunanka wai kai ɗin abokinsa ne. To ina jin sunan kuma na gane kai ne. Ta ce na bincika mata halayensa ne." Ta canza akalar zancen, ba haka suka yi da Jiddah ba, kawai dai shawara ta sake ne da zuciyarta. Ba yanzu ya kamata ta bayyana ma Farouk manufar Annur ɗin a kanta ba, gwara komai a bi shi a hankali, da sannu za a zo wurin. "Ok...ok thats nice." Ya faɗa da sauri don kar ta sake yo masa wata tambayar. "Har ɗazu ma mun tafi Maraɗi tare da su ai. Ƙawar tawa ce ta je gidan danginta a can, to sai muka tafi tare ya kai mu." Cikin mamaki ya ce, "Amnur ɗin?" "Ehh fa. Sai dare ma muka dawo, suka sauke ni har gida." "Gaskiya ba dai Annur nawa ba ne. Saboda tun safe muke tare da shi, har dare sannan ya tafi gida. Da alama dai wani ne ba shi ba." "Ina tababa fa." "Wallahi gaskiya nake faɗa miki. Tun safe muke tare ba mu rabu ba. Babu inda ya je, wata ƙila dai mai irin sunan ne." Gudun kar ta yi insisting ya gano ta ya sa ta ce, "To ina ji dai kam sunan ne ya zo ɗaya. Ƙila kuma wani Farouk ɗin ne daban abokinsa ba kai ba ne." Ƙwalwar banza irin ta ƴan shaye shaye kawai Bobby ya ce, "I think so. Lets back to business bae. Ina muka tsaya?" "Call me later, please. Am busy right now." "Please ki ɗauka idan na kira ki. Bana jin daɗin rashin ɗaukar nan da kike sometimes idan na kira ki." "Insha Allahu zan ɗauka. I promised!" Ta faɗa haɗe da gaggauta tsinke kiran, ta fuskanci Hadiza da fara'a. "Done." Ta furta bayan ta ajje wayar bisa cinyarta. Ta be lemon sprite, ta kurɓa a bakinta. "Me hakan ke nufi? Ya shafi aikin da muke ne?" Hadiza ta faɗa, saboda ita ɗin ba wai tana gane turanci ba ne. Bayan ta ajje lemon ta ce, "Sosai ma kuwa. Ina hankalinki ya tafi sanda muna wayar?" "Yana tare da ni." Ta faɗa a taƙaice. Cikin halin ko in kula Maryama ta ce, "Na gano abin da nake son sani. Ya bayyana min muhimmin abin da ya kamata na sani." Shiru ta yi Hadiza tana sauraron Maryama. Lemonta take sha a tsanake. "Ya shaida min duk yinin jiya yana tare da AIA. Ko kaɗan ba su rabu ba." "Waye AIA kuma?" Dafe kanta ta yi Maryama. Duk iya haƙurinta na jure tambayoyi Hadiza na neman ƙular da ita. Tambaya mara ma'ana, wacce ya kamata a ce ta san amsar. Guntun tsaki ta yi a bayyane, ta ce, "Ban san dalili ba, kamar dai ƙwalwar taki ba ta ja yanda ya kamata. Ko kaɗan ba na son hulɗa da mutum irin haka." Kallonta Hadiza ke yi cike da jin haushinta. Kawai dan ita ɗin kanta tana son sanin haƙiƙanin abin da yake faruwa ne, amma da tuni ta gwadawa Maryama halinta na tashanci, wanda take ma duk wani wanda ya nemi ya kawo mata wargi a lamurranta. "Ko kaɗan ba su rabu da Annur ba jiya. Suna a cikin garin nan. Kin ga kenan dai ba Annur ba ne kika gani a Maraɗi..." Miƙewa ta yi tsaye a fusace, cike da masifa ta ce, "Ke kar ki nemi miyar da ni shashasha mana! Ta ya da idona in ga mutum kuma ki nemi ƙaryata ni? Dan Bobby ya faɗa miki son ransa dole ne sai ya zama gaskiya? To ni dai ko ki yarda ko kar ki yarda na ga Annur a Maraɗi jiya. Ko tantama babu shi ne na gani." Miƙewa ta yi ita ma Maryama, ta dafa kafaɗar Hadiza, da murmushi ƙunshe a fuskarta ta ce, "Calm down Hadiza. I din't mean to hurt you. Dawo ki zauna mu ci gaba da maganarmu." Ba dan ta so ba ta koma ɗin ta zauna, tana mai tsananin jin haushin Maryama. "Ko kaɗan kar ki zaci wai na ƙaryata ki ne Hadiza. Wallahi na yarda da ke ɗari bisa ɗari. Na tabbata idan har ba ki ga fuskarsa ba, ba za ki ƙirƙira ba." Sai a sannan Hadiza ta ɗan ji sassauci a ranta. Amma fa har yanzu ba ta daina jin takaicin Maryama ba. "Am very confused. Baki ɗaya kaina a ƙulle yake. To ko dai Annur ɗin biyu ne wai? Ina nufin ko akwai mai irin kamanninsa ne? Idan ba haka ba, ya za a yi wanda ke Nigeria ya tafi Maraɗi cikin awanni shida, kuma a cikin awannin nan shida ya haukace, sannan zuciyarsa ta samu matsala? Kamar dai akwai alamar tambaya." Shiru Hadiza ta yi tana nazarin kalaman Maryama. To ko dai haka ɗin ne? Amma kuwa kamannin na su ta yi yawa. Ba su da bambanci ko kaɗan. "Ina so ki nutsu, ki kuma yi tunani mai kyau. Ya za a yi Annur ya haukace kuma ya warke cikin ƙanƙanin lokaci ba tare da wani makusancinsa ya sani ba? Idan ma hakan ta kasance, kina tunanin zaluciyarsa za ta samu matsala a iya wannan lokacin, har likita ya kula da shi, a ƙanƙainin lokacin nan? Kamar dai ciwon ya daɗe a jikinsa." Sai a sannan Hadiza ta faɗa kogon tunani. Tana ƙara tuna yanayin da ta ganshi. Haƙoransa baki ɗaya rinannu ne. Kayan jikinsa lalatattu, matattu. Sumar nan ta shi ƙazan ƙazan, duk ta cukurkuɗe. Fuskarsa duk ƙasumba, wadda ke ƙunshe da ƙazanta sosai. "Na yarda da batunki Maryama. Tabbas na amince, ba Annur ba ne na gani. Sai dai kuma kamar tasu har ta yi yawa. Ko kaɗan ba su da bambanci." Sosai Maryama ta ji daɗi da Hadiza ta fahimce ta. Ta ce, "Ina neman alfarmarki guda ɗaya tal, Hadiza." Laɓɓanta ta tsotsa duka biyun, bayan ta fiddo ta ce, "Ina jin ki." Gyara zamanta ta yi Maryama, ta ce, "Za ki iya raka ni mu je Maradi?" To fa! Tafiya Maraɗi ta taso. To ita Maryama ya za ta yi da gidansu? Ko iyayenta za su amince mata ta tafi Maraɗin? Ta wacce hanya za ta bayyana musu tafiyar ma? Ya za ta kaya idan ta haɗu da Modu? Ya za su yi ita da Fiddou idan sun haɗu? Akwai fa cakwakiya mai girma, wacce duk iya hasashemmu ba za mu iya cankowa daidai ba, dole sai dai alƙalamin marubuciyar ne kawai zai iya warware mana. Fatana dai a juri bibiyar marubuciyar, sannu a hankali za ta warware mana komai. Gaisuwa haɗe da jinjina ga ƴan Zauren Sadiya novels. Ina yinku, ina ƙaunarku, ina son ku all fi sabilillah! Thanks all for the love and care. Ina ƙaunar duk mai karanta littafin nan, har ma da wanda ba sa karantawa amma suna sharing ɗinsa. To wattpadians, gaskiya na raina yawan votes ɗin ku. Da alama dai kun fi son ƙananan pages. To hakan zan muku, idan kun shirya ma dogayen pages, sai in ga votes da yawa.🤓 RAZ Aminnan juna, jinjina ta musamman. Allah ya ƙara ɗaukaka amin. My Xarah BB, congratulations for the successeful completion of your novel named AMINAN JUNA. A very educated novel. Allah Ya ƙara miki ɗaukaka da nisan kwana. Fatan ana ba ma ɗammu kyakkyawar kula, yanda ya dace.😘 To my Sis, Rabiatu sk msh. We are still waiting for you fa. Kin san komai ba sai na bayyana ba.😸 Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:52 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!* ♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Msh _(Princess Amrah)_ *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* _Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler)_ 4⃣1⃣ Follow me on wattpad: PrincessAmrah Aunty Sady Jegal Khadeeja Candy Ashnur pyaar Miemie Queen Qurratul-ayn Easha md Fauziyya Ammany Lainat Meelah Adeel Wannan shafin na ku ne kyauta. Na gaishe ku, ina son ku, ina ƙaunarku all fi sabilillah. *** Cike da mamaki ta kalli Maryama, kamar dai ba haka ta so faɗi ba. A kan wane dalili za ta ce wai su tafi Maraɗi? Miye damuwarta ne ma wai? Tunda dai sun tabbatar da ba shi ɗin ba ne, a ganinta ai gwara kawai a bar maganar. Saurin barin tunanin ta yi ta miyar da hankalinta ga Maryama, ta ce, "Mu je Maraɗi?" "Kin ji me na faɗa ai. Ba kya buƙatar maimaici." Jinjina kanta ta yi Hadiza, ta sauke ajiyar zuciya haɗe da faɗin "Amma, me ya sa kike son mu je Maraɗi? A gani na ai babu wani abu da ya shafe ki da shi, tunda dai mun tabbatar ba Annur ɗin ba ne." Guntun murmushi ta saki Maryama, ta gyaɗa kanta, ta sake surɓar lemo tana faɗin, "Uhm...na san abin da nake..." Ta ƙarisa haɗe lemon daga bakinta, ta rufe gorar lemon ta ajje a bisa teburi. "...ke da kanki kika faɗi cikin halin da wancan ɗin yake ciki. A gani na tunda dai muna da halin taimakonsa, daga ni har ke ɗin, bai kamata mu zauna ba. Allah Yana jinƙan duk wanda yake jinƙan mutane. Ko bakya son samun lada ne?" Murmushin yaƙe ta yi Hadiza. Ba ta iya furta komai ba saboda yanda Maryama ta yi maganar, ba za ta iya cewa a'a ba. "Na san kina da halin taimakonsa. Ki fiddo kuɗi ni ma zan ƙoƙarta fiddowa, mu je Maraɗi mu taimaki bawan Allah'n, mu masa gata, dan Allah!" Shiru ta yi ba ta ce komai ba. Ta san tana da kuɗi kam tabbas, wanda ita kanta kai tsaye ba za ta iya faɗin adadin kuɗin da suke cikin account ɗinta ba, sai idan ta yi checking balance ne. "Ki taimaka, na yi alƙawari ni ma zan taimaka da dukkan abin da Allah Ya hore min. Baya ga haka, ina son ganinsa, ina son sanin ainahin waye shi? Ta yiu akwai abin da zai iya taimakona da shi." Babu abin da Hadiza ta fahimta a maganar Maryama ta ƙarshe. Kawai dai ta ce, "Ni ma na yi alƙawarin taimaka masa iya ƙarfi na." Kama hannunta ta yi Maryama, da murmushi ƙunshe a fuskarta ta ce, "Alhamdulillah! Na ji daɗi sosai da wannan. Allah Ya ba mu ikon taimaka masa. Allah kuma Ya ba shi lafiya. Ke kuma, Allah Ya fahimtar da ke gaskiya, ki daina irin wannan rayuwar da kike ciki." Ba ta ce amin ba, saboda ba ta da muradin hakan. Idan har ta bar zaman kanta a yanzu, ta tabbata Annur zai guje ta, saboda dama jikinta kawai yake so. Ita kuwa ba ta jin za ta iya jurar rashinsa a cikin rayuwarta. Ta jima tana ƙaunarsa, tun kusan shekaru biyar da suka gabata. Sai dai a wancan lokacin, wulaƙanta ta yake, yana cin mutuncinta. A ganinsa, shi ɗin ba ajinta ba ne. Amrah ce ta shi, ita kaɗai yake so. Duk wata mace ba ta gabansa, ba ya ganin ko wace mace sai Amrah. Rayuwarsa, tunaninsa da komai na shi ya ta'allaƙa ne ga Amrah. Wannan dalilin ya sa ya guji Hadiza, ya wulaƙanta ta sanda ta taɓa kai masa tallar kanta. Tun daga lokacin ta ƙoƙarta hana kanta shiga rayuwarsa, sai dai kuma duk wasu movements ɗinshi tana kula da su. A haka har ta ji labarin mumuwar rayuwar da ya faɗa bayan rasuwar Amrah, daga nan ne ita kuma ta sake kai masa kanta, take kuwa ya amince da ita, suka ci gaba da aikata alfahshar su. Tana cikin wannan dogon tunanin ne ta tsinkayo muryar Maryama na faɗin, "Idan na koma gida, zan yi tunani sosai, sai in tsayar da ranar da ya kamata mu tafi." Hadiza ta ce, "Bai kamata mu ɗauki dogon lokaci ba mu je ba. Yana cikin matsanancin tashin hankali, wanda ke buƙatar taimakon gaggawa. Na tabbata Fiddou tana kula da shi yanda ya kamata, sai dai matsalar ita ɗin ma ta kanta take. Rayuwarta abar tausayi ce, tana buƙatar taimakon ita ma kafin ta taimaki wani. "Haka ne. Insha Allahu ba zai ɗauki dogon lokaci ba. Daga yau zuwa jibi litinin, za mu tafi da izin Allah. Yanzu dai bara na tashi, Islamiyya zan tafi kar na makara. Tun ƙarfe tara ya kamata ina can, ga shi yanzu har kusan sha ɗaya da rabi na safe." "Ayyah! Allah sa dai kar a samu matsala a makarantar." Bayan ta miƙe Maryama, ta ce, "Babu matsala insha Allah. Da yake muna ta shirye shiryen walima ne." Ita ma Hadiza miƙewar ta yi, ta ce, "Haka ake so to. Mu tafi?" Kai Maryama ta ɗaga mata. Suka kama hanyar barin lambun. A bakin titi kowacce ta tsayar da tata napep ɗin, Hadiza ta wuce gidanta, Maryama kuma ta wuce Islamiyya. *** Tun bayan da ya farfaɗo aka dawo da shi ɗakinsa, ta ƙura masa idanuwa tana kallonsa da hawaye shimfiɗe a saman fuskarta. Shi kuwa in banda murmushi babu abin da yake yi. Sai butsu butsu idan ya kalle ta tana kukan shi ma ya ɓata fuskarshi, a dole ya ji haushin kukan da take yi. "Modu mi da kake haɗe ranka halan?" Ta ƙoƙarta shanye hawayenta ta masa wannan tambayar. "Ba ke ce ba..." Ya saki murmushi kuma, ya ce, "Kike dariya da ƙarfi." Kallon dolanci irin nasa kawai take. Sau da dama yakan ba ta dariya idan ya yi wani abun. Amma kuma tausayinsa da take ya fi yawa, shi yake hana ta darawar. "Modu kana da abin dariya wani lokacin. Yaushe kag ga na yi dariya a nan? Kana ciwon ne kuma zan yi dariya dan rashin imani? Kai ma hwa ka san ba zan iya ba." Yaƙe ya yi, ya ce, "Ai na san kina so na, kamar yanda nake son Amrah." Da mamaki ta kalle shi, farin ciki lulluɓe da zuciyarta. Yana son ta? Ta ma kanta wannan tambayar. Murmushi ta yi, ta ce, "Modu ashe dai ka san ina son ka. Na ji daɗi da kas san haka." Ɗaure fuskarsa ya yi kuma, ya harare ta kamar ba shi ne ya gama murmushi ba, ya ce, "Ni ba na son ki, Amrah nake so!" Ɓata fuskar ta yi ita ma. Har ga Allah tana jin haushin wannan Amrar da yake yawan ambata. Ba ta sani ba, shin tana raye ko ba ta raye? Duk da haka dai tana kishinta. Sau da dama zuciyarta kan raya mata cewa babu wanzuwar Amrah a doron ƙasa, kawai dai surkulle ne irin na taɓaɓɓi. Sai dai kuma a wasu lokutan, wani sashe na zuciyarta yakan ba ta tabbacin akwai Amrah, sai dai inda take ɗin ne ba ta sani ba, kuma ita ɗin mai muhimmanci ce a rayuwar Annur. Sai kuma ranar da likita ya ba ta tabbacin Amrah ba ta rasa nasaba da larurar Annur, saboda yawan ambaton sunanta da yake, da kuma yanda ake tanƙwara shi ta hanyar ambatar sunanta. Share sabon hawayen da ya fito mata ta yi, ta sauke nannauyar ajiyar zuciya, tana mai matuƙar tausayinsa, da kuma makomarsa idan har ba a samu kuɗin siyan maganin nan ba. "Kin ji haushi na ce Amrah nake so ko? Ita ɗin ma na san tana so na. Mu yi auremmu mu haifi ƴaƴammu..." Ya rufe fuskarsa alamun ya ji kunya. Murmushin ƙarfin hali ta ƙirƙiro, ta miƙe haɗe da faɗin, "Kana jin yunwa, na sani. Bari in tai in samo ma abinci." Kafin ta fara ajje takunta ta ji sallamar Dr. Huzaif. Kallo ta bi shi da shi fuskarta ba yabo ba fallasa. Sallama ya yi ta amsa, sannan ta daidaita masa kujerar da zai zauna, ita kuma ta fasa fitar da za ta yi, dan ta san akwai abin da yake tafe da likitan. "Ashe ya farka." Ta Jiyo muryarsa, bayan ya zare glasses ɗinsa yana bin Modu da kallo yana murmushi. "Ehh, bai jima da tashi ba." Ta faɗa a hankali, cikin sanyin murya. "Ni za ki kira dama da kika miƙe?" Ya tambaye ta yana ƙoƙarin ciro takarda daga aljihun lab court ɗinsa. Ba ta ba shi amsa ba, kanta sunkuye yake a ƙasa, haka kawai ba ta ƙaunar haɗa ido da shi. Ita dai ta tsane shi, tun daga sanda ta fahimci rashin iya maganarsa. Ga shi dai likita, amma ko kaɗan bai san yanda zai yi magana ya kwanatarwa mutane hankali ba. Har da son ganinshi ba ta yi, dan dai kawai ya zame mata dole ne. Sassauci ɗaya take samu a wannan tsanar da ta masa, da yake ƙoƙarta kula da Modunta. Gyran murya ya yi a karo na uku, saboda sai faman miƙa mata takardar yake amma sam! Hankalinta ba ya gare shi, tana can tana faman tunani. Da saurinta ta miƙa hannu ta karɓi takardar, ta buɗe cikin sanyin jiki. Magungunan ne a rubuce guda biyu, da kuma gargaɗin kar ya ringa amfani da duk wani abu mai cholesterol, saboda har da shi ne ya masa yawa a zuciyarsa. "Ki tabbatar an siyo magungunan nan, daga yau zuwa gobe nake so ya fara amfani da su." Kanta kawai ta ɗaga masa, hawaye na ƙoƙarin fara fita daga idanuwanta. "I repeat, ki tabbatar an siyi magungunan nan, rayuwar giɗe na cikin matsala matuƙar ba a siya wanga magunguna ba. Ciwon zai iya kai wa har inda bai kai a yanzu ba." Hawayen da take ɓoyo ne suka gangaro a daidai wannan lokacin. Ita ba ma ta san yanda za ta yi ba. Shin sata za ta yi ta samo wannan kuɗin? Ko kuwa kanta za ta miƙa da maza domin ta samu kuɗin siyan magungunan nan? Kanta ta gyaɗa alamar a'a, ko kaɗan ba ta yarda da wannan shawarar ba. Sam! wannan ba mafita ba ce. To miye abun yi? Miye mafita? Share hawayenta ta yi. Abincin da za ta nemo masa ya ci ma take tunani, tun ma kafin a kai ga kuɗin siyan maganin. "Akwai inda na masa order'n abinci, sau biyu kullum a wuni. Na biya kuɗin duka, na tsawon sati biyu. Na hwaɗi musu irin abincin da za a ringa kawo masa ɗin, saboda na san indai dan ta ke ne, za a iya samun matsala, dan da ganinki ke ma ba ki kula da kanki ba, bare kuma a yi maganar kula da wani, wanin ma kuma mai larurin zuciya." A fusace ta ɗago kanta ta kalle shi. Hawayen da take ɗin ma tayawa suka yi cak! Takaicinsa take. A kan me zai ringa jifar ta da duk kalaman da suka fito daga bakinsa? Dan yana likita kawai sai ya raina mata hankali? Talauci hauka? Ai ba kanta farau ba, kuma ba kanta ƙarau ba. Da sauri da sauri zuciyarta ke bugawa. So take ta maida raddi amma wani sashi na zuciyarta yana hana ta. Ba ta gama tunanin yanda za ta yi da shi ba ta ji ya yi murmushi, ya ce, "Kar ki bar giɗe bai sha maganin nan ba. Idan kin san ba ki da kuɗin saye nai tun wuri ki hwaɗi min, a san yanda za a yi da shi. Da ganin ki hwa..." "Wai kai wane irin mutum ne, wanda ke hwaɗin magana duk yanda rai nai yas so? Halan dai kaina hwarau talauci? To bari ka ji in hwaɗi ma, kai ba ka isa ka wulaƙanta ni ba. Kuma magani ka riƙe ba a so, da yardar Allah zan sai mai magani daga yau zuwa gobe. Abincinka ma ka riƙe ba a buƙata." Ta ƙoƙarta shanye hawayenta daga nan. Tana tunanin duk maraici ne ya ja mata hakan. Inda iyayenta suna raye shi har ya isa ya wulaƙanta ta haka? Ya ma isa ya kalli idanuwanta ya faɗa mata wannan maganganun? Gyaɗa kanta ta yi, cikin fushi ta ce, "Kana cin arziƙin Modu ga shi nan. Wallahi dan dai kana kula da shi ne, da tuni na hwaɗi ma maganar da har ka mutu ba za ka taɓa mantawa da ni ba." Cikin halin ko in kula ya murmusa, shi kam da alama dai ranshi ba ya ɓaci. Sai ya gama guma wa mutum, sai kuma ya dawo yana dariya. Sam! Bai da damuwa. Wanda ma ya biye shi shi ke cikin matsala, dan shi kam zai ɓata maka rai amma bai san ya yi ba. "Abinci kam na riga da na yi magana, na tabbata ba da daɗewar nan ba kina ganin an kawo mai na dare. Magani kuma tunda kin ce ke ba matsiyaciya ce ba do Allah dai a ƙoƙarta saye nai yau." Ya ƙarisa maganar yana dariya ya bar ɗakin. Wurin zama ta nema ta zauna tana kuka sosai. Duk da ta san ba ta da hanyar siyan maganin, ta gwammaci hakan a kan ta zauna Dr. Huzaif yana cin mutuncinta. Bayan kamar minti talatin sai ga wani matashi tafe ɗakin, hannunshi riƙe da robar take away. Gaishe da Fiddou ya yi ta amsa. Ya miƙa mata ledar abincin cikin girmamawa ya bar ɗakin. *** Tun bayan dawowarta daga islamiyya take tunanin mafita. Ta ma rasa ta hanyar da za ta ɓullowa lamarin. Ya za ta yi Mama ta amince da buƙatarta? Shin ta wace hanya ma za ta bi wurin faɗa mata taimakon da take son yi? Allah Ya sani, tana son taimakon bawan Allah. Tana son tabbatar da zarginta; na kasantuwar wani bawan Allah mai kama ɗaya da Annur. Tabbas ba za ta iya tabbatar da zarginta ba, har sai ta haɗu da wancan ɗin, sannan. Rashin samun mafita ya sa ta kiran Jiddah a waya. Babu ɓata lokaci Jiddah ta ɗauka, a nan Maryama ke sanar da ita duk yanda suka yi da Hadiza. Ta ƙare da faɗin, "Na samu na shawo kanta har za ta taimaka da kuɗi, amma ni ban san ta inda zan ɓullowa Mama da maganar ba. Na sani, kuɗi ba matsala ba ne, saboda Abba yana so ma ya ji wani mabuƙaci, don ya taimaka masa. Samun damar tafiyar dai ita ce matsala." Shiru suka yi su duka biyun, Jiddah na tunanin shawarar da za ta ba ƙawarta, Maryama kuma zullumi kawai take, kar lokaci ya ƙure mata har iyayen nata su kwanta, kuma ga shi gobe take son tabbatar ma Hadiza da tafiyarsu jibi litinin. Bayan shiru na wani lokaci da suka yi, Jiddah ta ce, "Ga shawara..." Ta ci gaba da tsara mata zance ƙasa ƙasa, wanda duk ƙwaƙwaf ɗin mutum ba lallai ya ji me suke faɗi ba. Bayan Jiddah ta gama maganar Maryama ta saki lallausan murmushi wanda sai da haƙoranta suka bayyana. Shi ya sa take son Jiddah, take kuma alfahari da ita. Yana da wuya a wannan zamanin ka samu ƙawa irin Jiddah; wacce za ta so ki saboda Allah, ta mayar da damuwar ki tamkar tata, ta ƙaunace ki tamkar ke ɗin jininta ce. "Na tabbata idan na faɗi haka su Mama za su amince. Allah Ya ga zuciyata, taimako nake son yi. Zan kuma roƙe sa gafara, insha Allahu Zai gafarta min." Jiddah ta ce, "Da yardar Allah kuwa. Ki tafi yanzu, kar ki ɓata lokaci dan Allah. Ki yi duk yanda na ce miki, kar ki nuna wata alama ta rashin gaskiya, wadda za ta sa a gano ki. Allah na tare da mu, kuma Shi Zai taimaka mana da ƙarfin mulkinSa." Da wanann ƙwarin guiwar da Jiddah ta ba ta suka yi sallama. Ta miƙe bisa takunta, cikin tafiyarta ta rashin kuzari ta doshi hanyar falo. A yi haƙuri da wannan. Da gaske fa dramar Dr. Huzaif da Fiddou na ba ni dariya yasin. Wato dai Dr. Huzaif tsokanar faɗa, Fiddou kuma saurin ɗaukar zafi.😁😂 Maman labyb ina yin ki, ina son ki, ina kuma ƙaunarki fisabilillah👐 Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:53 PM] Princess Amrah✍🏻💞: 🅰MRAH NAKE SO!♥ (Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi.) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) NAGARTA WRITERS ASSOCIATION Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (sickler) 4⃣2⃣ Follow me on wattpad: PrincessAmrah *** Zazzaune ta tarar da Mama da Abba, sai Muhammad zaune daga gefe yana game da ipad ɗinsa. Ƙarisowa ta yi ta zauna a ƙasa, murmushi shimfiɗe a fuskarta ta ce, "Sannunku da hutawa Abba." Da fara'a shi ma mahaifin nata ya ce, "Yauwa Maryama sarauniyar mata. Yanzu ko muke maganar saukar ku." Mama ta karɓe da, "Invitation cards ɗin duka an bugo, kin gan su can ajiye a tv stand. Idan akwai wanda za ki kai ma, sai ki ɗiba ki kai gobe. Akwai wani abu kuma da kike so?" Hannunta ta ɗora a gefen goshinta alamar tunani, ta ce, "Mama an canza kalar hijab ɗin anko, wai ya yi shige da uniform ɗin wata islamiyya. To da dai wasu sun ce kar a canza, saboda ƙurewar lokaci, mafi rinjaye dai sun tsaya a kan a canza ɗin. A taƙaice dai an canza shi yanzu haka." Mama ta ce, "Babu damuwa. Sai kuma me?" "Uhm...ban san ko ya ake ciki ba wurin masu buga takardun nan." "Yanzun nan Abbanku ya kira Shamsu, an gama jotters da tissues, biro ce kawai ba a gama ba, amma wai aikinta kaɗan ne, cikin daren nan za su ƙarƙare komai, gobe da safe a je a karɓa." Maryama ta yi murmushi mai nuna zallar farin ciki, ta ce, "Lallai sun cika alƙawari ko." Mama ta ce, "Gaskiya kam. Dama gobe muka yi da su." Dariya Abba ya yi, ya gyaɗa kansa ya ce, "Kuna da aiki. Ku da ba a je an tabbatar sun yi ko ba su yi ɗin ba ne har kun fara faɗin suna da cika alƙawari. To ba girin girin ba dai..." Mama ma murmushin ta yi, ta ce, "Kuma fa haka ne. Amma dai na tabbata za su cika alƙawari, da yardar Allah. Shi kenan abin da kike so?" Ƙoƙarin danne rashin gaskiyarta ta yi, da ƙyar ta haɗiyi yawu, ta zaƙulo magana daga ƙasan maƙoshinta, "Mama dama ina son sanar da ke wani abu, taimakon da nake son na yi." Ta dakata daga nan, tana son jin martanin Maman tata, kafin ta shiga cikin zancen kai tsaye. "Wane irin taimako kike son yi, Maryama? Allah sa dai lafiya." Shiru ta ɗan yi na wani lokaci, kafin ta zaro magana daga can cikin maƙoshinta, muryarta can ƙasa, tana son yin maganar yadda za ta tabbatarwa Abba da Mama iyakar gaskiyarta. "Uhm...dama akwai wata ƙungiya da nake, ƙungiya ce ta taimakon al'ummar musulmai, maza da mata. Ana bin duk asibitoci domin duba wanda ba su da lafiya, a ba su tallafi, a taimaki duk wani mai buƙatar taimako." Ta ɗan jinjina maganar da za ta yi a gaba, kafin ta ɗora da, "Tunda ake yi ban taɓa zuwa ba, sai dai ina bayar da gudummowa daga nan inda nake. Sau tari idan na karɓi kuɗi daga wurin Abba, transfer ɗinsu nake kai tsaye zuwa ga account ɗin shugaban foundation ɗin. To kuma yanzu wata tafiya ta taso, Maraɗi za a je, mun ji labari cewa wai asibitocinsu na gwamnati suna da buƙatar taimako, shi ya sa aka yanke shawarar kai musu ziyara, mu taimaka musu." Tana rutsewa ta guntse bakinta, tana sauraren martanin Mama, dan ta san halinta sarai, ita ɗin ba ta son wargi. Daga can ta tsinkayo muryar Abba, ya ce, "Banda abinki Marayama, ina ke ina shiga irin wannan foundations ɗin? Ba wai na ce shigarsu tana da aibu ba, sai dai sam! Bai kamace ki shiga a yanzu ba, yanzu da kike kan yin karatunki. Ina laifin dai ki bari ki gama, gudun rabuwar hankalinki?" Shiru ta yi tana saurarensa, ya ci gaba da, "Kuma ai ba mutuncinki ba ne tafiya har Nijar, ba tare da iyayenki ko wani na ki ba. Ki dai sake duba wannan lamarin." A fusace Mama ta ce, "Har ma sai ka tsaya kana mata lallaɓi? Ita ai ta sani, ta san daidai, ta kuma san bana son wannan shirmen. Ni ai Maryama ban ma san sanda kika fara yin wani abu, ba tare da kin faɗa min, ko kin nemi shawarata ba. Kuma ki gaggauta fita daga ƙungiyar, tun ban ɓata miki rai ba." Hawaye ta ji suna bin kumatunta. Ta ma kasa furta komai, kanta sunkuye a ƙasa. Ji ta yi Abba ya ce, "Zan miki transfer na 10k yanzu, sai ki tura musu, ki ba su haƙuri kan cewa ba za ki samu damar zuwa ba." "To Abba, na gode." Tana gama faɗin haka kawai ta tashi da saurinta ta bar falon, ta nufi nata ɗakin. Gadonta ta haye tana kuka sosai, dama jikinta ya ba ta, sai da ta yi wannan tunanin. Amma yanzu ita ya za ta yi? Me za ta faɗawa Hadiza? Har ga Allah tana son taimakon bawan Allah'n, ta na matuƙar son ta gan shi. Tunani ta fara a ranta; sun yi plan ɗin farko ya lalace, babu nasara. To ga shi wannan ma tun ba a je ko'ina ba ya lalace. Ko dai ƙaryar da take ma iyayenta ne? Akwai fa alamar tambaya a wannan lamarin. Tunda take a rayuwarta, ba ta taɓa ɓoyewa mahaifiyarta wani abu ba, sai daga fara case ɗin nan. Ko dai hakan ne ke bibiyarta, ya sa suka kasa yin nasara har yanzu? A yanda mahaifiyar Amrah ta sanar da ita, ko kaɗan Amrah ba ta kasance mai ƙarya ba, komai za ta yi to iya gaskiyarta za ta yi shi, koda kuwa hakan na nufin rashin farin ciki a gare ta. Me ya sa ba za ta zama mai koyi da halayen Amrah ba? Me ya sa ba za ta zama abar alfahari ga nata iyayen, kamar yanda na Amrah suke alfahari da Amrah ba? Share hawayenta ta yi ta jawo wayarta, ta latsa kiran Jiddah. Bugu biyu ta ɗauka tana faɗin, "Su Mama sun amince ko? Ai dama na san ba za su ƙi amincewa ba." Shessheƙar kukan da Jiddah ta ji Maryama na yi ne ya dakatar da ita daga maganar da take yi. Cikin lallausar murya ta ce, "Maryama kar dai ki ce min ba a dace ba." Cikin kuka Maryama ta ce, "Ba a dace ba Jiddah. Sam! Wannan shawarar ba ta ɓullar da ni ba. Jiddah ban taɓa yiwa Mamana ƙarya irin haka ba, na tabbata Allah ba zai ƙyale ni ba. Ba zan taɓa samun nasara ba matuƙar ina ci gaba da yi ma iyayena ƙarya." Cike da damuwa Jiddah ta ce, "To fa! Abu bai yi daɗi ba kuwa. Kuma yanda na faɗa miki ɗin haka kika yi?" "Haka na yi Jiddah. Abba dai ya turo min kuɗi wai na tura musu, in faɗa musu ba zan samu zuwa ba. Ita mama cewa ta yi ma na fita daga ƙungiyar baki ɗaya." Ta sake fasa wani kukan, zuciyarta raunane, tana mai neman mafita. Cikin kwantar da hankali Jiddah ta fara mata magana, a yadda take maganar, tamkar ta na a gaban Maryama ɗin ne. "Ya isa haka please! Kukan ai ba zai amfana miki komai ba, dan Allah ki daina." "Jiddah ban san ya zan yi ba, zuciyata ta riga da ta kamu da son ganin wancan bawan Allah'n. Ban san dalili ba, amma nake ji a jikina akwai wani ɓoyayyen al'amari a tattare da shi. Jiddah ko kin san cewa zargin da nake shi..." Dakatar da ita ta yi Jiddah, ta ce, "Na samu shawara, amma fa mai haɗarin gaske, ba lallai ba ne ta zama hanyar ɓullewa." Maryama ta gaggauta faɗin, "Allah sa dai ba wata ƙaryar za ki saka ni yi ba, dan wallahi na riya a raina ba zan kuma yi wa iyayena ƙarya ba, sai dai in komai zai lalace." Ajiyar zuciya ta sauke Jiddah, ta ce, "Ni kaina na gano babban kuskuren da muka tafka a karo na biyu, wanda duk hakan ne yake jawo tangarɗa a plans ɗinmu. Shi ya sa dama na faɗa miki, wannan kam ba lallai ba ne a yi nasara." "Ina jin ki Jiddah, go on." "Me zai hana kawai ki tunkari Mama da maganar, ki faɗa mata gaskiya? A gani na hakan kawai zai iya zame mana mafita, idan ta amince shi kenan, ida ma ba ta amince ba sai mu haƙura, kawai ki fita daga al'amarin, duk yanda Allah Ya tsara daidai ne." Cike da yaƙini Maryama ta ce, "Haka ne Jiddah, tabbas na yi wannan tunanin ni ma. Kawai mu daina ɓoye ɓoyen." "Tabbas kuwa. Yanzu yadda za a yi, kawai bari gobe da safe idan na yi shirin islamiyya in biyo ta nan, ni zan tinkari Mama da maganar, na san ta sigar da zan mata, kuma insha Allahu za ta amince." "I trust you Jiddah. Allah Ya kai mu goben." "Ameen. Sai da safe. Please ki cire damuwa daga ranki, Allah Ya na tare da mu, kuma Ya ga zuciyoyinmu taimako muke son yi." "Na gode ƙwarai. Sai da safe." Kashe wayoyin suka yi su duka. Duk da damuwar da Maryama take ciki, haka kawai take jin nutsuwa a cikin zuciyarta. Hankalinta ya ɗan kwanta yanzu kam. Tabbas ƙarya fure take ba ta da ɗa. Mai gaskiya ba ya taɓa shiga shakku, a duk inda zai je. *** Tun daga lokacin da boka ya lalata true love ɗin da Annur ya faɗa, sai ya samu sauki, hankalinsa ya kwanta sosai, yanzu kam ba shi da sauran fargaba, tunda ya ga Dady'nsa ya koma yanda yake masa a baya. Ko ya je aiki ko bai je ba, iyayensa ba sa masa faɗa, ko kaɗan ba sa takura shi. Sai wata irin ƙauna da take ƙara shiga a tsakaninsu. Mugun halinsa kuwa ƙara ta'azzara kawai yake. Shaye shaye da mugun bin matansa, sai abin da ya ci gaba. A wannan lokacin kam babu soyayyar Maryama ko kaɗan a zuciyarsa. Sam! Ya ma manta da ita a doron ƙasa. Dama tuni aka fidda masa Jiddah daga zuciyarsa, Maryamar dai ce abun ya gagara, har sai da boka ya yi aiki a kanta. Sigari yake zuƙa, yana jin yanda zuciyarsa ke masa daɗi, rayuwarsa na cikin kwanciyar hankali. Sosai yake jin duk wata gaɓa ta jikinsa na ƙarfafa masa guiwa wurin aikata alfahsharsa, ta hanyar ingantacciyar lafiya da yake da ita. Wayarsa ce ta yi ƙara, ya ɗan karkaɗe tokar sigarin, haɗe da jawo ta a jikinsa, yana duba mai kiran nasa. Sunan da ya gani ne ya sa shi gaggauta ɗauka, yana murmushi ya ce, "Abokina ya dai?" "Normal guy. Kana ina ne?" "Ina gida. Akwai damuwa ne?" Daga ɗaya ɓangaren Bobby ya ce, "Babu damuwa. I just wanna see you right now." "Akwai damuwa kenan." Annur ya faɗa. "Ehh to, wata damuwa ce a tattare da ni, tun ina ɓoyo dai na ga ya kamata ko kai na sanar da kai, gudun samun matsala." Ajje karan sigarin ya yi a bisa ɗan ƙarfen da yake ɗorawa, cike da damuwa ya ce, "Me yake faruwa da kai guy?" "Tarin nan dai da nake yawan fama da shi ne, ka sani ai. To abun yake damu na sosai, ba kaman da ba, yanzu fa har da jini nake fitarwa daga maƙoshina. Na rasa ta ina matsalar take." Zaro idanuwa ya yi Annur, tamkar yana gaban Bobby ɗin ne, ya ce, "Matsala fa babba ba ƙarama ba guy. Me ya sa kake zaune da ciwo ba ka faɗawa kowa ba? Ai ya kamata a ce an je asibiti." Bobby ya ce, "Dalilin da ya sa na faɗa maka ɗin kenan. Na tabbatar idan na tinkari Abbana da maganar, ba zai tsaya saurare na ba, zai ce shegen shaye shayen da nake ne na jawowa kaina masifa. Ka san halin dai Abba sarai." Dafe kanshi ya yi Annur, ya ce, "Ka kwantar da hankalinka. Na tabbata ba wani abu mai girma ba ne. Gobe da safe zan zo in ɗauke ka, sai mu je asibiti a duba ka. Ka kwantar da hankalinka, everything will be okay." "Thank you very much guy. Am very grateful." "You are always welcome. Amma ka kiyaye guy, don't drunk today, har sai an gano ta inda matsalar take." "Ok guy." Suka yi sallama. *** kallon sa ta yi da murmushi ta ce, "Zan tai gida in dawo, mi kake so in taho ma da shi?" Hannunsa ya ɗora bisa haɓarsa alamun tunani, ya kuma sauke hannun, ya yi dariya sosai haɗe da faɗin, "Alawa mai tsinke." Ya ɗan karkace kansa, hannuwansa duka biyun ya rufe fuskarsa, wai shi a dole ya ji kunya. "Aikam zan taho ma da alawa mai tsinke. Bari in tahi, ka yi min addua ka ji?" Ta nufi barin ɗakin. Har ta kai bakin ƙofa ta ji muryarsa ya ce, "Idan an dake ki ki rama. Kar kuma ki ma kowa kuka, ni ne nan zan shigar miki. Ni jarumi ne." Ya jinjina hannunshi alamun shi ɗin mai ƙarfi ne. Murmushi ta yi ta ce, "Banda abunka Modu, halan wa zai bugu na?" "Yo su mana." Ya marairaice mata fuska tamkar ya ga ana dukanta ɗin ne. Da fara'a a fuskarta ta ce, "To jarumina. Duk wanda yab buge ni ina tahowa in hwaɗa maka, Moduna jarumi." Sosai ya ji daɗin ɗorasan da ta yi. Ta fice daga ɗakin murmushi shimfiɗe a saman fuskarta. Koda ta isa gida da ɗar-ɗar ta shiga. Tsoron shiga gidan take, gudun tashin hankali. Duk da yake dai yanzu ta ji huɗubar da Hadiza ta mata, sam! Ba ta jin za ta iya haƙuri da abubuwan da Aunty Sahiya ke mata. Ta gaji, haƙurin da take ne ya sa take mata yanda ta ga dama, har ƙannenta ke taya ta. Cikin wata irin murya ta yi sallama. Tun a zaure ta gane Yayanta ya dawo, saboda mashin ɗinsa da ta gani ya faka. Farin ciki ta ji ya ziyarci zuciyarta, gani take tamkar baƙin cikinta ya zo ƙarshe, a tunaninta zai ba ta kuɗin da za ta siyawa Modu magani, koda ba duka ba ne. A tsakar gida ta same su, ya zauna bisa tabarma, ga kular abinci a gabansa yana ci. Da murmushinsa ya kalle ta, ita ɗin ma ta sakar masa. Ɗan uwa rabin jiki. Take ta ji wani irin daɗi ya lulluɓe ta. Duk da dai yana biyewa matarshi suna ƙin kyautata mata, hakan bai hana shi nuna yana ƙaunarta. Sunkuyawa ta yi har ƙasa ta gaishe shi. Ya amsa sannan ya ba ta izinin zama a bisa tabarmar. "Giɗe zuba abinci ki ci. Halan daga ina kike? Tun ɗazu ina ta ma Sahiya magana ta ƙi hwaɗi min inda kika tahi. Sai dai ta ce wai in bari har in kin ga dama kin dawo, sai ki hwaɗi min." Babu haufin komai Fiddou ta hau ba shi labarin duk abin da ke faruwa. Da zaman da take yi asibiti tare da shi Modu ɗin. Sosai ya tausayawa Modu. Ko kaɗan ba ta tsammani hakan daga gare shi ba. Ba ma ta zaci zai yarda da ita ba. "Wayyo bawan Allah! To yanzu halan ya ake ciki? An samu kuɗɗin maganin?" Daɗi ta ji sosai, ta yi tsammanin ko kuɗin zai ba ta, hakan ya sa da sauri ta ce, "Ba a samu ba Yaya. Do Allah dai ka taimaka muna idan kana da hali." Mamaki ƙarara a fuskarsa ya kalle ta. Lallai ma Fiddou. Shi ɗin ta kanshi yake. Biɗar kuɗi ya je kuma ba wani abun kirki ya samu ba. Jarinsa na takalmi tuni ya karye, saboda rayuwar yau da gobe. Ban so tsayawa a nan ba, dole ce ta sa; ina fama da mura da ciwon kai, zazzaɓi duk a lokaci guda💆 da ƙyar ma na samu yin wannan ɗin. Please include me in your prayers. I love y'all fisabilillah. Da gaske ne fa, duk abin da aka saka ƙarya a cikinsa ba ya tasiri ko kaɗan. Musamman ma kuma a ma iyaye ƙarya, duk yadda ake ganin kamar an yi nasara, tabbas a ƙarshe za a ga akasin haka. Ramin ƙarya ƙurarre ne. Bari mu gani, ko za ta dace a wannan karon? Ku dai cigaba da bibiyar marubuciyar, sannu a hankali za a zo wurin. Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:53 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 4⃣3⃣ follow me on wattpad: PrincessAmrah *** Sanye take da doguwar hijabinta mai hannu, ta uniform ɗin Islamiyyarsu. Sannu a hankali take taku, tana jin yanda gabanta ke tsananta duka, fargaba ta dabaibaye mata kaf illahirin jiki da ruhinta. A hankali ta yi sallama, cikin raunanniyar murya, mai nuna zallar damuwar da take cikinta. Amsa sallamar ta ji an yi, aka ƙara da faɗin, "Shigo ciki ina zuwa." Bisa ɗaya daga cikin kujerun da ke jere a falon ta zauna, ajiyar zuciya take saukewa, lokaci zuwa lokaci. "A'aha a'aha! Yau Hauwa Jiddah ashe ke ce." Murmushi ta ƙirƙiro da faɗin, "Wallahi kuwa ni ce Mama. Allah sa dai Maryama ba ta riga da ta tafi ba." Bayan Mama ta zauna ta ce, "Duk yau ko motsinta ban ji ba. Na rasa me yake damun wannan ƙawar taki, shez not in her mood, tun jiya." Shiru Jiddah ta yi tana taunar leɓonta na ƙasa, sai rarraba idanuwa take, ta sunkuyar da kanta ƙasa. "Ta zo min da wani batu ne jiya, wanda sam! Hankali ba zai iya ɗaukarsa ba. Ban san me ya sa yarinyar nan baki ɗaya ta sauya min ba, duk wasu shawarwarinta ta daina tunkarata da su, damuwarta ba ta tinkara ta da ita, tun wasu makonni da suka shuɗe." Cikin ƙarfin hali Jiddah ta ɗago kanta a wannan karon, ta samu zaƙulo sanyayan kalamai daga bakinta. "Mama dan Allah idan na ce zan miki wani bayani za ki fahimce ni?" Gyara zamanta ta yi Mama, ƙyam ta ɗaura idanuwanta ga Jiddah, ta ce, "Zan saurare ki Jiddah, zan kuma fahimce ki insha Allahu." Ƙasa ta dawo ta zauna Jiddah, ta ajje jakarta daga gefe, ta ce, "Mama na san Maryama ta ba ki labarin Amrah ko?" "Tabbas ma kuwa. Labarin da ya girgiza ni, ya taɓa zuciyata, ya zauna min a cikin zuciya har yanzu." "Mama akwai abubuwan da Maryama ta yi kuskuren ɓoye miki, ba ta sanar da ke su ba, dangane da labarin Amrah." Ko kaɗan Mama ba ta ɗauke idanuwanta daga fuskar Jiddah ba, hankalinta da komai nata ta tsayar da shi ga Jiddah, sosai take neman ƙarin bayani. "Mama akwai Annur..." Ta kwashe komai ta sanar da Mama; tun daga farkon soyayyar Annur da Amrah, har zuwa lokacin da Amrah ta rasu, Annur kuma ya haukace. Ta faɗa mata kaf munanan halayen da Annur ya faɗa, tun bayan sanda ya warke daga hauka, har zuwa wannan lokacin. Ba ta ɓoye mata taimakonsa da suka yi attempting yi a karon farko ba, da kuma silar ƙaryar da Maryama ta musu jiya. A ƙarshe ta fasa kuka, tana ƙoƙarin yin magana Maryama da ke laɓe bakin labule ta fito daga ɗakinta, ta ce, "Mama ina zargin ba ainahin Annur ba ne a gidansu, wallahi wannan mahaukacin ne real Annur, shi ne masoyin Amrah!" Ba mama kaɗai ba, hatta da Jiddah sai da ta ɗago kanta da mamaki ta kalli Maryama, ko kaɗan ba ta yi wannan zaton ba. Sai yanzu ma abun ya zo mata. Haƙiƙa biri yai kama da mutum. Ita sai ma yanzu zahirin labarin Amrah ke dawo mata. Cewa tana ganin wani mai kama ɗaya da Annur, wanda har ya taɓa sace ta. To ko dai da gaske shi ɗin ne? Kenan bai warke daga haukan da yake tun bayan mutuwar Amrah ba? Ko kuwa dai ya warke wata cutar ce daban? Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke Mama. Baki ɗaya ma kanta ya ɗaure. Wani ɓangaren zuciyarta tausayin Annur ne ya gama mamaye ta, wani ɓangaren kuwa tunanin mafita kawai take. Shin za ta amince ma ƴarta tarar wannan riskin ne, ko kuwa za ta hana ta aikata taimako? Hannunta ta sa ta dafe kanta. A hankalin ta shafo shi har bisa fuskarta, ta ce, "Maryama ta yi kuskure tun farko, na rashin sanar min da wannan al'amarin. Ba a ɓoyewa iyaye matsala irin haka, abokin kuka ba a ɓoye masa mutuwa. Kin sani, daga ni har Abbanku ba za mu hana ki taimako ba, musamman ma ga mutum irin Annur, wanda yake da buƙatar taimakon. Yanzu da kika ɓoye mana halin da kike ciki, inda a ce shi wancan mugun ya miki wani abu, ya kike gani? Dan Allah Maryam kin mana adalci kenan? Yanzu za ki so a ce 'yarki ta cikinki ta miki haka? Ya za ki ji idan hakan ta kasance a gare ki? Sam! Ban ji daɗi ba Maryam, ban taɓa tsammanin akwai abin da zai rusar da alƙawarin da ke tsakaninmu, na sanarma juna damuwarmu ba." Kneel down ta yi Maryama, hawaye take sosai, ta matso kusa da Mama, cikin muryar kuka ta ce, "Na sani, ni ɗin mai laifi ce Mama. Dan Allah ki gafarta min, wallahi na rasa ta inda zan fara faɗa miki aikin da nake shirin yi ɗin ne, gudun kar ki hana ni. Amma wallahi na nadama, yanzu kam na gane kurena, na tabbatar cewa ashe dai ƙarya fure take ba ta da ɗa. Duk wanda ya kasance yana aikatata, to tabbas babu shi babu cin ribar komai na rayuwa. Duk wasu tsare tsare na shi za su lalace. Allah Ya sani na nadama, na yi da na sani Mama, wallahi ba zan kuma yi ba. Amma dan Allah ba dan halina ba, ki taimaka ki bar ni na ci gaba da wannan aikin ladar da nake son yi. Insha Allahu babu abin da zai faru sai alkhairi..." Ba ta kai iya inda take son ta tsaya ba, kuka ne dai kawai ya ci ƙarfinta, ya hana ta ƙarisa zancen nata. Ganin haka ya sa Jiddah ta ɗora da, "Kin ga Mama ita kanta waccan Hadizar sai da Maryama ta shawo kanta, yanzu haka ta alƙawarta bin Maryama, su je har can Maraɗin tare, su taimaka ma bawan Allah'n, sannan su tabbatar da gaskiyar lamarin. Yanzu mama idan har Maryama ba ta samu zuwa ba, muna tsammanin Hadiza ma za ta je? Mama dan Allah a dubi wannan lamarin, taimako ne, jihadi nn mai girma, kuma mai matuƙar lada. Allah ne kaɗai Ya san ladar da za mu samu, daga mu har ku." Datse haƙoranta ta yi bayan ta kai nan, alamun dai ta kai aya a nata zancen kenan, wanda shi ne Maryama ta so ta ƙarisa faɗi, sai kuka ya ci ƙarfinta, wanda ya gagare ta ƙarisa zancen. Murmushi Mama ta yi, ta gyaɗa kanta cikin barkwanci ta ce, "Wani abu sai yaran zamani. Ku fa a dole wayo kuke son ku min ko?" Jiddah ma murmushin ta ƙirƙiro, ta ce, "Mama ba wayo ba ne, neman taimako ne kawai." "To na ji. Sai ku tashi ku tafi makaranta kar ku makara." Maryama ba ta miƙe daga kneel down ɗin da ta yi ba, a hakan cikin kuka ta ce, "Mama ai ba ki faɗa mana kin amince ko ba ki amince ba. Na tabbatar Hadiza na son jin wani abu daga gare ni, ina gudun kar ta ji ni shiru ta canza ra'ayinta." "Ya isa haka to daina kuka. Tashi ku tafi na ji, zan ma Abbanku magana." Murmushi sosai Jiddah ta yi a wannan karon, ba tun yanzu ta san rayuwar gidan su Maryama ba; sosai babansu yake da sauƙin kai da bin ra'ayin yaransa, musamman ma idan abin da ya shafi farin cikinsu ne, matuƙar dai bai saɓawa sharia ba. Dama Mama ce kaifi ɗaya, idan har ta ce haka to hakan, yana da wuya ta kuma canza magana, saboda ita ɗin ko kaɗan ba ta wasa da tarbiyyar yaranta. "Yauwa Mamammu, a lallaɓa mana shi da kyau dan Allah. Insha Allahu zai aminc..." "Na ma amince." Suka jiyo muryar Abba na fitowa daga hanyar ɗakinsa, tare da ƙoƙarin isowa tsakar falon. Murmushinsa ya faɗaɗa, "Ba kuna magana ne a kan zuwa Maraɗi ba? Na ji komai ai. Ko ni na bada goyon baya ɗari bisa ɗari a je a taimaki bawan Allah'n. A masa duk abin da ya dace. Idan ma kuna ga kamar zama can ɗin ba zai yiu ba, za ku iya kawo shi nan, sai a nemi likitan ƙwalwa da na zuciya su duba shi, idan Allah Ya ba shi lafiya na san za mu ji komai daga gare shi. Zan bada gudummowar mota cike da mai, da kuma dreba ya kai ku har Maraɗi." Tsalle Maryama ta buga haɗe da rungumar Abbanta, abin da ba ta saba ba. Ko a mafarki ba ta taɓa tsammanin za ta iya ma Abbanta haka ba. Sai yanzu ta yarda, ashe dai daɗi da farin cikin kan saka mutum aikata har abin da bai yi niyya ba? "Na ji daɗi sosai Abba. Sai yanzu na ƙara tabbatar da ashe dai na tafka babban kuskure, na gudar iyayena da wata buƙata tawa. Ina sonku sosai iyayena. Wallahi na ma rasa ta ina zan fara bayyana muku murnata." "Ta hanyar ƙara jin tsoron Allah kawai. Idan har kika kasance haka, to tabbas kin nuna mana farin cikinki na wannan lamarin, zan kuma ci gaba da yi miki addua, Allah Ya ba ku ikon taimakonsa, Ya cika muku burinku." Komawa ta yi ga Mama, hawayen farin ciki take, wanda ba ma ta san sanda suke fitowa ba. Ji take kamar an mata bushara da gidan Aljannah. "Thank you so much Mamana. Allah Ya miki albarka Ya raya min ke." Dariya suke su duka a wannan lokacin, lallai ma Maryama, ji wata addua da ta ma Mama kamar wata ƴarta ta cikinta. "Na ji to amin. A tashi a tafi kar a makara. Kamar ma na ji motsin Mallam Ya'u, da alama ya dawo daga kai Hammad Islamiyya." Bayan ta miƙe ta share hawayenta, ɗakinta ta nufa domin sanyo hijabinta, ta kuma ɗauko jakarta. Ko kafin ta dawo sai da Jiddah ta daɗa yi musu godiya sosai, ta kuma shaida musu cewa da banda ita ne tafiyar, amma za ta ƙoƙarta sanar ma iyayenta yau, insha Allahu tare za su tafi. Ta zaɓi su tafi taren ne kawai don hankalin su Mama ya ƙara kwanciya da tafiyar. *** Tsawon lokaci suke zaune gaban teburin likitan, tun bayan da aka ma Farouk Sardauna chest xray suke zaman jiran sakamako. Likitan na zaune da farin medical glasses a idonsa, ya mayar da hankalinshi baki ɗaya ga rubutun da yake yi. Wani mutumi ne ya shigo bayan ya ƙwanƙwasa ƙofar an ba shi izinin shigowa. Hannuwansa riƙe suke da takarda mai faɗi, wadda hoton ƙirjin yake a ciki. Bayan ya miƙa ta ga likita cikin girmamawa ya fita, likitan ya ɗago kanshi daga rubutun, a hankali ya zaro hoton daga cikin envelope ɗin. Duddubawa ya hau yi, kimanin tsawon mintuna goma yana rubutu, kafin ya ce, "Na yi mamaki. Hoton ƙirjinka lafiya lau yake, bai bayyana kowace matsala ba. Kenan dai ko kaɗan tarinka bai da nasaba da ƙirjinka, zargin da nake na pneumonia ko kaɗan ba ita ba ce. Saboda idan ita ce za ta bayyana a hoton nan. Tabbatuwar ko mura babu a ƙirjinka kenan." Ya ɗan dakata daga nan, yana fiddo iska daga cikin bakinsa. Glasses ɗin nasa ya cire, ya ci gaba da faɗin, "Gwaje gwaje biyu ne ya kamata a maka yanzu; tuberculosis test, sai kuma a yi hoton cikinka baki ɗaya. Dole a gaggauta yinsu, matuƙar tari ya fara yin irin wannan tsananin, wanda har ake fitar da jini to lallai ya ta'azzara. Amma kar fa ku damu, insha Allahu komai zai daidaita. Gano ciwon dai ne aiki, da zarar aka gano shi, ka hau turbar magunguna, za ka ga komai ya zama tamkar ba a yi ba." Wani irin zazzafan huci ya fiddo daga bakinsa Bobby, tausayin kansa yake. Yau kimanin watanni uku kenan yake fama da wannan mugun tarin, sai dai bai ta'azzara sosai ba sai a cikin kwanaki huɗu da suka gabata. Tun daga sannan ko barcin kirki ba ya samun yi. Da zarar barci ya ɗauke sa to sai tari ya farkar da shi. Cikakken minti talatin ba ya jerawa yana barci. Ba kuma wai ya sha naganin tari ya samu sassauci har barci ya ɗauke sa ba, sam! Ba ya masa aiki. Ya riga ya zama addicted da shan shi, ta kai ga ba ya ma saka shi barcin, sai dai kawai ya kai shi wata duniyar, mai cike da sama da ƙasa. "Ga wannan takardar, da ita za ku je a yi gwaje gwajen. Ku tabbatar an yi su nan da ranar talata, yau Sunday gobe Easter Monday babu aiki, a nan kuma wanda zai maka ɗin ba ya nan, in short, an ɗau tsawon lokaci ma ba a yi ba a nan. Ku daure ku je a yi, idan an maka ɗin sai ku kawo min result ɗin." Miƙewa suka yi su dukansu jiki babu ƙwari. Ko a tuberculosis ɗin aka tsaya wani babban laruri ne, mai wuyar magani. Ga shi kuma ɗaukarsa ake, babu wuya na kusa da mutum ya kwasa. Babu wanda ya iya cewa kowa uffan. Sosai Annur yake tausayin abokinsa Bobby. Ko ba komai damuwar Farouk damuwarsa ce. Kamar yanda ta shi damuwar take ta Farouk Sardauna. *** Tunda sassafe ta tashi ta hau shirye shiryen tafiya. Ta kira Hadiza cewa ta zama ready, nan ta minti arbain ta fito bakin titi za su ɗauke ta. Jiddah ma sun yi magana, ita za su fara ɗaukowa kafin su tafi ɗauko Hadiza. Ko karyawa ba ta yi ba ta fito, sanye take da baƙar abaya mai adon cyan, ta yafa mayafinta, sai jaka da takalminta duka cyan colour. Tana fitowa falon Mama ta ce, "Maryama ba dai har tafiya ba, ba fa ki karya ba." Cike da ɗoki ta ce, "Ba na jin yunwa Mama. Za mu biya ta crispy mu yi take away mu tafi da shi, idan mun ji yunwa sai mu ci." Gyaɗa kai ya yi Abba. Da murmushi a fuskarsa ya ce, "Ke dai zakwaɗi ne kawai. Sai a yi a tafi ai. Mallam Ya'u tun ɗazu ya iso, yana zaman jiranki." Muhammad ne ya fito daga ɗakinsa sanye da pyjamas light brown. Yana miƙa da muryar barci ya ce, "Yaya Maryama ina za ki je?" "Zan yi tafiya ne Hammad. Include me in your prayers, please!" Matsowa ya yi daf da ita ya ce, "Ina za ki je haka Yaya Maryama? Ba fa ki sanar min ba." Harararsa ta yi cikin wasa, ta kama hannuwansa duka biyu, ta ce, "Naughty you. Kawai dan zan yi tafiya dole sai na sanar da kai? Yaron nan fa ka raina ni ma." "A'a fa Maryama. My boy is not a naughty boy, he's a good boy, right?" Ya kalli Muhammad yana masa murmushi. Kai ya ɗaga ma Abban nasa, ya ce, "To Abba ka ce mata ta tafi da ni." "Abba ka gani ba? Da gaske yaron nan ya raina ni fa. In banda rigima ko wanka bai yi ba sai ya ce wai a ce na tafi da shi?" Mama ta murmusa ta ce, "Rabu da ita yarona. Super market za mu je anjima idan ta tafi. Just let her go, wayo za mu mata." "To Yaya Maryama a tafi. Daike iyayena suna so naaa!" Ya ƙarisa maganar da jan ƙarshen, yana mata gwaliyo haɗe da rugawa ya ɓoye bayan Abba. "Uhm...kanka dai ake ji yaro. Abba barin fita." A tare Mama da Abba suka ce, "To Allah Ya tsare hanya." Mama ta taso ta matso inda take. "Allah yana tare da ke, Maryam. Insha Allahu zai kare mana ku, za kuma ku yi nasara a kan wannan nannauyan aiki da kuka fara. Ki tafi cikin aminci, adduata tana tare da ke, everywhere you go. Please contact me or your father when you need any help, okay?" Kai ta ɗaga Maryama, da murmushi a fuskarta ta ce, "Insha Allahu. Thank you very much Mama." Ta fita daga ɗakin. Sai da suka fara biyawa suka ɗauki Jiddah sannan ta kira Hadiza cewa sun taho ta fito bakin titi. Ko da suka isa kuwa ta fito ɗin, su kawai take jira suka tafi. *** Tun bayan shigarsu asibitin take rarraba idanuwa, zuciyarta ƙagare take da ganin mara lafiyan, idanuwanta na burin yin tozali da shi. Hadiza ce gaba sai Jiddah da Maryama biye da ita a baya. Babu mai furta komai a cikinsu. Suna isa bakin ƙofar ɗakin Modu suka ringa jiyo maganganun Fiddou da Dr. Huzaif. Masifa yake mata da iya muryarsa. Iya ɓacin rai yau ya shige shi. Dr huzaif bai kasance ɗaya daga cikin mutane masu saurin ɓacin rai ko kuma ɗaukar zafi ba, sai dai kuma yau a yanayin yanda yake faɗan ya isa ya tabbatarwa kowa cewa ransa ya hasala. "Ba sau ɗaya ba ba sau biyu ba na hwaɗi miki a gaggauta siyan maganin nan. A ƙarshe har tambayarki nai yi akwai kuɗin siyan maganin? Baƙar magana kika yi min. Kuma sai yanzu in zo ki kama ce min wai ba a samu kuɗi ba? Halan ban hwaɗi miki zuciya tai tana iya kai matakin da ba za mu so ba? Siyan magungunan nan ne kaɗai zai kawo ma giɗe sassauci, to kuma ke banda rashin kunya babu abin da kika ƙware da shi. To ni kam iyakar abin da zan iya yi kenan, magani kuma idan kin ga dama kar a siya, I did my best, and leave you the rest." Ya kamo hanyar barin ɗakin. Kiciɓis ya yi da su Hadiza, hakan ya sa shi ɗan kauce musu, yana neman barin ɗakin. Cikin azama Hadiza ta ce, "Dr. Dan Allah ka yi haƙuri. In dai kuɗin magani ne ga su a siyo a ba shi. Ka ma Fiddou uzuri, wallahi ta kanta take ita ma." "Biyo ni na rubuta miki, a gaggauta siyo masa su yanzu." Ba ta ko bi ta kan su Maryama ba, ta bi bayan likitan kawai suka fice daga ɗakin, hankalinta a tashe. Tun bayan shigowarsu hankalinsu yake gare shi. Zaune yake ya naɗe ƙafafuwansa kamar mai zaman tahiya. Ya fuskanci daidai ƙofa sai faman yaƙe yake. Cikin dariya ya ce, "Na faɗa miki ki ringa ramawa. Haka kawai sai yaita miki masifa?" Sai kuma ya yi shiru, take hawaye ya fara kwaranya daga idanuwansa. "Halan missa kake kuka Modu? In dai dan ka ga ina yi ne to ni ma na daina, ka gani ba? Na share hawayen." Ta ƙoƙarta yin murmushi. Mamaki bai gushe daga fuskokin ƴan matan biyu ba. Da gaske babu bambanci tsakanin Annur da Modu. Sai dai kuma kallo ɗaya duk wani mai ƙwalwar kirki zai ma Modu ya tabbatar da cewa ya jima a cikin halin taɓin hankali. Saboda har idanuwansa sun juye, irin na mahaukata sosai. Komai nasa abun ƙyama ne; kayan jikinsa, fuskarsa, gashin kansa da komai ma. "Ka tsaya da kukan nan ge, walle na yi shiru hwa." Murmushi ya yi kuma, cikin wata murya kamar mai hankali ya ce, "Amrah ta taɓa faɗa min a duk halin da na tsinci kaina na zama mai haƙuri. Ko tana raye ko ba ta raye, in rinƙa tunowa da wannan maganar, ta ce wai hakan zai sa na samu riba mai girma a rayuwa." Sai kuma ya ci gaba da yaƙe haƙoransa. Mutuwar tsaye kawai su Maryama suka yi. 'Amrah!?' Su duka biyun suka jinjina a ƙasan ruhinsu. 19th Aughust 1987 BAMA, BORNO STATE. A yi haƙuri na ji na shiru kwana biyu, abubuwa da dama suka sha kaina, kuma dai har yanzu ban gama samun ƙarfin jikina ba. Dan Allah ina barar addua'arku, Allah Ya biya mana buƙatummu na alkhairi baki ɗaya. Yanzu za ku fara jin salon labarin yana sauyawa; za mu koma yinsa kwan-gaba kwan-baya, sai kun ajje hankalinku sosai sannan za ku fahimce shi. Fahihtarsa na ɗaya daga cikin warwaruwar labarin. Don haka ɗaure ɗamararku, the game has just started.😀 ummiieeterh jinjina da fatan alkhairi. Ƙaunarki nake fisabilillah! Ba sai na faɗa muku me ya dace ku yi ba a yayin da kuka karanta ko wanne peji. Na san kun sani. Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:53 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 4⃣4⃣ Follow me on wattpad: PrincessAmrah *** Kallonta yake cike da so da ƙauna, idanuwansa ƙyam a bisa fuskarta, yana jin yadda soyayyarta ke azalzalar zuciyarsa. Sosai yake tausayinta, rayuwarta, da komai nata abun tausayi ne. "Dadyn Nadrah wannan irin kallo haka, ai sai ka sa mutum ya ƙware." Hannunsa ya sa ya shafo fuskarta, da yatsunsa ya taɓa hancinta da murmushi shimfiɗe a bisa fuskarsa. "Ba zan taɓa gajiyawa da daina kallon matata Suhaila ba, komanta burge ni yake; murmushinta, kallonta da komai ma. Kin ga kenan za ki shekara kina ƙwarewa in dai don ina kallonki ne." Ya ƙarisa maganar tasa da faɗaɗa murmushin nasa. "Yauwa, ni kam Dady akwai maganar da nake so mu yi; batun yaran nan ne, ya kamata a ce sun shiga makaranta haka nan, musamman ma Nadrah da ta fara girma, ya ci a ce ta jima da shiga makaranta." Hannunsa na dama ya ɗora a bisa haɓar Suhaila, cikin shauƙin so ya furta, "Na jima ina wannan tunanin, sai dai kuma abin da nake ji taɓarɓarewar karatunsu, kin ga yanzu haka maganar transfer ake mana, shi ya sa ba na son aikin federal wallahi, babu wuya sai a lalata karatun yaro, saboda yawace-yawace." "Huh!" Ta sauke ajiyar zuciya, ta ce, "Duk da haka dai ai ba za mu tsaya jiran inda za a mayar da kai ba, waye ya san sadda za su ɗauke ku ɗin?" "Gaskiya ne. Bari insha Allahu ranar Monday zan binciki makaranta mai kyau sosai, ina son gina ilimin yara sosai, babban burina shi ne yarana su ginu bisa turbar karatu, both na boko da na islama ɗin." "Haka ne Dady. Allah Ya kai mu to." Ta yi shiru daga nan, ta dafe ƙasan mararta da take ji yana mata ciwo sosai ba kaɗan ba. "Suhaila ya dai?" Ya tambaye ta bayan ya dafe mata marar tata, yana kallon cikin idonta don jin amsar da za ta ba shi. "Babu komai Dady, kawai dai marata ce nake ji tana ɗan katsa min, amma ba sosai ba." Ta ƙoƙarta ƙirƙiro murmushi. "A'a Suhaila, ki faɗa min gaskiya fa, ko haihuwar ce?" Hararar wasa ta masa, da murmushi ta ce, "Dady akwai sauran lokaci fa, edd ɗina fa sai nan da sati biyu zai cika." "Hmm! Suhaila kenan. Don an ce expected day of delivery ai bai zama dole a ce sai a ranar za ki haihu ba. Su ma kansu hasashe ne, ba wai sun tabbatar ba ne. Kuma za a iya haihuwa mako biyu kafin edd ɗin, ko kuma mako biyu bayan edd ɗin, babu yanda ba ta kasancewa. Don haka..." Salatin da ya ji Suhaila na yi ne ya sa ya kasa ƙarisa zancensa, cije laɓɓanta ta yi tana jin yanda ciwon ke ƙara nuƙurƙusarta, kodai haihuwar ce da gaske? "Suhaila na faɗa miki haihuwa ce wannan, ki tashi kawai mu tafi asibiti. Nadrah! Saddiqa!" Ya ƙwala musu kira. Nadrah ce ta yo gaba sai Saddiqa biye da ita a baya. "Nadrah kawo hijabin Momy, asibiti za mu tafi, ba ta jin daɗi ne." Da saurinta Nadrah ta nufi uwar ɗakar Suhaila domin ta ɗauko mata hijabin, Saddiqa kuwa tambayoyi kawai take jerowa Dadynta, cewa baby boy za a siyo musu? Baby girl? Dady a tafi da ni... Ko saurarenta bai yi ba Dady, ya gaggauta karɓar hijabin da Nadrah ke miƙo masa, cikin kaɗuwa yake zira mata hijabin, har yana mayar da ƙasa sama, sai da Nadrah ta taimaka masa. "Nadrah yi sauri ki ɗauko ma Saddiqa mayafi ke ma ki ɗauko na ki." Cikin kaɗuwa ya yi wannan maganar, yana ɗaukar mukullin motarsa daga bisa tv stand, wanda yake haɗe da na gidan baki ɗaya. Fita ya fara yi ya buɗe motar, ya wangale gate ɗin gidan sannan ya dawo ciki da sauri, ya taimaka ma Suhaila ta miƙe tsaye, hannunta dafe da mararta har yanzu ba ta saki ba. Ganin kamar dai tafiyar tata ba za ta mata daɗi ba, ya sa ya cicciɓe ta da iya ƙarfinsa, ya kai ta bayan motar ya kwantar, lokaci zuwa lokaci yana yi mata sannu. Komawa ya yi ciki ya ɗauko kayan jarirai adadin wanda suka fara tarawa, kamar sun san cewa haihuwar za ta zo yanzu, sun siya komai, sai dai haɗa su ne wuri guda kawai Suhaila ba ta yi ba. Kwaso su ya yi da yawa ya jera a cikin riyo, ya fito daga ɗakin. Yaran ya umurta cewa su isa bakin motar, shi zai rufe gidan sannan ya fito. A daburce yake aikata komai, dakiya kawai ya yi da bai rafka kuka ba. Dama haka yake yi a duk haihuwar da Suhaila za ta yi, sosai take shan wahala kafin ta haihu, kuma kusan a tare suke jinyar, dan ba ya zuwa ko ina har sai ta haihu. Cikin motar ya dawo ya tada, sannu yake ta maimaita mata, sanda zai yi reverse ma sai da ya ƙura mata ido yana ƙara jin tausayin mata a zuciyarsa, lallai mata abun a tausaya musu ne, abun a ma uwa mace biyayya, shi ya sa manzon Allah SAW ya ambaci kyautatawa uwa mace har sau uku sannan ya ambaci uba namiji. Gyaɗa kansa ya yi cikin ƙarfin hali ya ƙirkiro murmushi, ganin yanda yaran ke kuka riris, mamansu da ba ta da lafiya. "Ya isa haka Nadrah, ke fa babba ce bai kamata kina kuka ba. Ke da ya kamata ki rarrashi ƙanwarki Saddiqa amma ke ce ma za ki zama Oganniya?" Shessheƙar kukan suke har a lokacin, sosai suke tausayawa mahaifiyarsu. Bayan ya fitar da motar waje ya dawo ya rufe gate ɗin, a gaggauce ya koma cikin motar ya tayar suka lula sai FMC da yake aiki. Da suka isa ba wani ɓata lokaci sosai aka yi ba, kasantuwar a can take awo, kuma shi ɗin staff ne a asibitin, yana ɗaya daga cikin manya manya a Pharmacy. Ɗakin haihuwar aka nufa da ita, wata nurse kuma ta karɓa riyo ɗin da ke hannunsa, shi kuma ya zauna daga can nesa, kasantuwar ba a barin maza matsowa kusa da labour room ɗin. Tagumi ya rafka da duka hannuwansa, Nadrah na daga gefensa na dama, sai Saddiqa a gefensa na hagu, ta kasa daina kukan, duk da yarintarta. A can labour room kuwa wahala sosai Suhaila take sha, banda salati babu abin da take yi. Ta sani, ta san cewa tana shan wahala sosai a wurin haihuwa, amma fa tunda take ba ta taɓa shan wahala irin wannan ba. Sabbatu take tana furta a kira mata Dady ta roƙi gafararsa, ta san cewa tata ta zo ƙarshe, mutuwa za ta yi. Sosai mid-wives ɗin ke bata baki, arniyar ciki na furta "push." Musulmar kuma na faɗin "yi ta addua, haihuwar na kusa." Haka dai sukaita fama har suka ɗauki kusan awa biyu da rabi babu haihuwa. A daidai wannan lokacin ne kuma aka kawo wata shuwa da ciki ƙerere, da ƙyar take tafiya, naƙuda ta ci ƙarfinta ita ma. Nan da nan masu karɓar haihuwar suka raba kawunansu, wasu na wurin Suhaila da suka fara tunanin ko ba za ta iya haihuwa da kanta ba sai an yanka ta, wasu kuma na kan wannan shuwar kyakkyawa, wadda a shekaru ba za ta wuce sa'ar Suhailar ba. A daidai lokacin da arniyar nurse ɗin ke furta, "Lemmi go and call the doctor, it seems like there's a problem..." Kukan jaririn da ta jiyo ne ya dakatar da ita daga maganar da take yi, ta ɗaga kanta ta hango ashe wannan shuwa ɗin ce ta haihu, hakan ya sa ta sake juyowa ga Suhaila, a daidai sadda kan jinjirin ya gama fitowa. Da taimakon abokiyar aikinta suka ƙarisa fiddo jinjirin, ɗan ƙarami da shi, kamar wani pre-tamp (Yaron da bai isa haihuwa ba, amma kuma ya wuce bakwaini. Ɗan kimanin watanni takwas kenan). Juya kanta ta yi ta sake ganin waccan shuwa ɗin tana sake yin wata naƙudar, alamun da sauran wani yaron a cikin cikinta kenan. *** A hankali cike da mamaki suke takunsu, ba su san sanda suka ƙariso gaban gadon ba su duka biyun. Kallonsu Fiddou ke yi ita ɗin ma mamaki bai gushe daga fuskarta ba, tana son sanin su ɗin su waye, kuma me suka zo yi a ɗakin? Tunawar da ta yi cewa tare suka shigo da Hadiza ya sa ta dakatar da wannan tunanin, da alama dai ƙawayen Hadizar ne, tunda suka zo tare. "Sannunku da zuwa." Ta furta cikin sanyin murya, tana ƙoƙarta ƙirƙiro murmushi a fuskarta. "Yauwa dai, sannu." Jiddah ta faɗa, Maryama kam ko samun damar amsa gaisuwar Fiddou ba ta yi ba. Tabbas ikon Allah ba ya taɓa ƙarewa. Al'amarin Allah mai girman gaske ne. Tunda take a rayuwarta, ba ta taɓa ganin kama irin wannan ba. Da ba don ta tabbatar cewa Annur na Katsina ba, da ita kanta ta yi irin na Hadiza, ta ce lallai shi ne wannan a gabanta. Sai dai kuma ta tabbatar cewa ba shi ɗin ba ne, tsantsar kama ce kawai da suka yi. "Modu ga baƙi nan sun zo duba ka hwa. Ka yi musu magana." Fiddou ta furta tana kallon Modu da murmushi. Dariyar yaƙe ya yi ya ce, "Ai na gan su, su ne wanda za su kai ni wurin Amrah?" Sai a sannan Maryama ta ɗan murmusa, ta kalle shi da fara'a ta ce, "Ka dai shirya ma tarar ta ko?" Kai ya ɗaga mata da sauri, alamar ehh, yana ƙoƙarin saukowa daga bisa gadon. "A'a Modu..." Ta gyaɗa masa kai tare da ambatar sunan da ta ji Fiddou ta kira sa da shi. "Kai zamanka, ai ba ka da lafiya, idan ka ji sauƙi ba sai mu je ba?" Kuka ya fasa a wannan lokacin, duk wanda zai zo ya masa maganar Amrah sai dai ya masa ƙarya cewa zai kaisa wurinta amma ba a kaisa ɗin, ga Maryama ma yanzu tana neman yi masa haka. "Ba za ki kai ni ba, haka kowa yake yi min. Amrah nake so, Amrah nake son gani, na san ita ma a duk inda take tana can tana tunanina, tana son ta ganni a kusa da ita..." Kuka wiwi kamar ba shi ne ya gama dariya ba. Jinjina kai ta yi Maryama, lallai hakan ya sake tabbatar mata da zarginta. Ko tantama babu wannan shi ne real Annur, wancan ɗan iskan fake Annur ne, wallahi ba shi ba ne, ta faɗa a ranta. Cikin dabara Jidda ta fara rarrasar Modu, tana faɗin, "Wannan karon kam ba ƙarya za mu maka ba, ba za mu taɓa tafiya mu barka a nan ba, ƙafarmu ƙafarka. Amma fa sai idan ka yi shiru, ka daina kukan nan." Shanye kukan nasa ya yi Modu, ya ɗan dafe ƙirjinsa, saitin da zuciyarsa take. Ji yake ciwo mai tsanani, a duk sanda zai tuna da wani abu da ya shafi Amrah haka zuciyarsa ke masa zafi da raɗaɗi, ya ringa jin ƙwalwarsa tana juya masa, na tsawon lokaci kafin ya dawo daidai. Haka suka ringa rarrasar Modu, cikin hikima da dabara har suka shawo kan Modu, ya cigaba da fara'arsa kuma. "Halan ƙawayen Hadiza kuke?" Suka tsinkayo muryar Fiddou ta yi wannan maganar daga inda take zaune. Jiddah za ta yi magana kenan Maryama ta yi saurin yi mata signal alamun ta yi shiru, shirun kuwa ta yi ta zurawa Maryama idanuwa tana son sanin ainahin abin da take nufi, da hana ta maganan da ta yi. "Uhmm...mu ƴan uwan Annur ne..." Tun Maryama ba ta rufe baki ba Fiddou ta zaro idanuwanta cike da mamaki tana kallonta. Me suke nufi? "Shekara da shekaru kenan ana nemansa ya ɓata, ba kuma a san inda yake ba. Duk iya inda za a duba an duba amma ba a ga Annur ba. Da haka har ya ɗauki tsawon wannan lokacin da aka riga aka cire rai da ganinsa. Kwatsam! Sai ga Hadiza ta zo nan, to ita kuma ta sanshi, shi ne fa da sauri ta kai rahoto gidanmu, iyayenmu basa nan ne shi ya sa sai mu muka zo." (Dole dai sai an yo ƙaryar nan🙊) Kuka ta fasa Fiddou da ƙarfi, wanda ita kanta ta rasa gane ko na menene. Shin na farin cikin samun dangin Modu da aka yi ne, ko kuwa na baƙin cikin lokacin rabuwarsu ya yi? Ta sani, dama akwai irin wannan ranar, wacce ita kanta tsumayenta take, cike take da ɗokin zuwanta. Amma kuma me, ba ta san ya rayuwarta za ta kasance a lokacin da Modu ya tafi ya barta ba. Ba ta san ya rayuwarta za ta kasance ba matuƙar babu Modu a cikinta. Ƙaunarsa take, ta yi nisa a begensa. Ashe haka so yake? Ta tambayi kanta. Ita da soyayya ta tashi kama ta sai ta faɗa ga mahaukaci, wanda ba ta san asalinsa ba, wanda ko kaɗan bai kasance yana ƙaunarta ba, wata yake so daban, wadda da alama sun shaƙu iya shaƙuwa. Rayuwarsa da komai sun ta'allaƙa ne ga waccan ɗin, wacce take yawaita jin yana ambatar sunanta. Wacce a kullum yake begen kasancewa a tare da ita dare da rana. Duk yanda yake aikata wani abu idan ta so ya daina sai ta ambaci wannan suna yake dainawa. Haka zalika ko wani abu take so ya yi to dole sai ta ambaci wannan sunan zai aikata shi. Ita kam soyayya ba ta mata adalci ba, ko kaɗan ba ta kyauta mata ba. Da ƙyar ta samu dawowa cikin hayyacinta. Hawayenta ta samu da wahala ta share, sai dai kuma wasu ne ke ƙara gangarowa a bisa fuskarta. So take ta tsaida kukan, amma abu ya gagara. Shikenan yanzu za a raba ta da Modu. Ba ta san sanda ta ɗora hannuwanta duka biyun a bisa kanta ba. Kuka take sosai, tana gyaɗa kanta, tana jin yanda zuciyarta ke mata zafi, take tafarfasa ta kowanne lungu da saƙo da ke cikinta. Kallonta suke da mamaki. Ita fa wannan baiwar Allah'r wacece ita? Me ya sa take kuka sosai haka kawai dan sun ambaci su dangin Modu ne? Cikin ƙarfin hali Maryama ta ce, "Baiwar Allah please ki daina kuka. Bakya so danginsa su zo ne?" Cikin shessheƙar kuka Fiddou ta ce, "Babban muradina shi ne in ga ƴan uwan Modu sun zo. Abin da na jima ina jira kenan. Giɗe na tabbata zan yi kewar Modu, zan jima ina tunani nai, walle ba zai taɓa hita daga raina ba. Soyayya nike mai ta tsakani da Allah, mai cike da tsantsar tausayi da jinƙai. Ban san me ya sa ba dama, tunda kuka shigo ɗakin gabana ke hwaɗuwa, na rasa dalili. Sai yanzu nag gane dalilin, ashe dai tahiya za ku yi da Moduna..." Kuka sosai ya ci ƙarfinta. Ita kanta mamakin kanta take. Babanta da mamanta duka sun rasu, sun bar duniyar baki ɗaya. Amma tafiyar da za a yi da Modu ji take tamkar da rayuwarta za a tafi. Tausayinta sosai suke a wannan lokaci. Lallai so cuta ce, cuta mai matuƙar girma kuwa. "Ke ni bana sonki, Amrah nake so! Na sha faɗa mata cewa ita kaɗai zan so, ba zan taɓa son wata mace ba bayan ita. Hehe!" Ya kama dariyarsa, yana wasa da haɓar gyalen Jiddah da ke zaune gefensa. Gyaɗa kanta ta yu Fiddou. A duk lokacin da Modu zai faɗi makamancin haka, tafarfasa zuciyarta ke yi. Tana ƙara kunna wutar tsanar Amrah, tsanar sunan Amrah, da duk wata magana da za ta fito daga bakin Modu a daidai wannan lokacin. Sosai take jin kanta na mata ciwo, zazzaɓi ke saukowa a jikinta. Gangar jikinta na tsananta karkarwa, zuciyarta na tsananta tafasa, idanuwanta na daɗa kawo ruwa, tsayuwar da take kuwa ƙafafuwanta sun gagara ɗaukar gangar jikinta. Duƙawa ta yi a gabansa, ta riƙe ƙafarsa ta dama, cikin muryar kuka ta ce, "Na san ba ka so na Modu, ba ka taɓa ƙaunata ba ko kaɗan. Amma do Allah dai ina biɗar alhwarmarka, kar ka mance da ni idan ka tahi, kar ka mance da Fiddousi a rayuwarka. Ka ajje a zuciyarka cewa Fiddou mai ƙaunarka ce, mai matuƙar ƙaunar Modu duk da bai kasance mai hankali ba. Ka ajje a birnin zuciyarka cewa babu mai ƙaunarka sama da ni, babu wanda nake ƙauna sama da kai, ba kuma za a samu ba har abada!" Ta haɗa kanta da guiwa, sosai take zubar da ƙwallanta, kamar wacce aka sanarwa mutuwar wani mai muhimmanci a rayuwarta. Da sauri Maryama ta tallabo Fiddou, a hankali ta zauna kusa da ita, ta ɗora kanta a bisa cinyarta, tana ɗan bubbuga bayanta kaɗan kaɗan, tana ƙara jin tausayinta a cikin zuciyarta. Muryar Modu suka jiyo ya ce, "Ke ki daina dariya, wai don na ce bana sonki ne kike ta faman yin dariya? To ki daina, ki yi kuka, na ji ina sonki, amma na fi son Amrata" Ya girgiɗa kanshi, irin dai yanda mahaukata ke yi. Sosai Maryama ke ƙara tunawa da labarin da Maman Amrah ta bata. Irin soyayyar da suka yi, yanda suka yi yarintarsu, soyayyarsu da komai, shaƙuwarsu da matuƙar tausayin junansu. Sadaukarwar da Annur ya yi na rayuwarsa, lokacinsa, farin cikinsa da komai ma saboda Amrah. Wannan wace irin ƙauna ce? Soyayya ta tsakani da Allah kenan, wacce kuɗi ba sa gusar da ita. Soyayya da zuciya ɗaya, wacce babu kwaɗayi ko son abun dubiya a cikinta. Ga Annur dai ya jima da haukacewa, amma ya kasa mantawa da soyayyarsa da Amrah, wacce duka silar haukan nasa ma mutuwar Amrah ne. Ita kanta Maryama hawayen take, sosai take ƙara tunowa da labarin Amrah. Tausayin Annur take, sosai tausayinsa ke shiga cikin ɓargo da jininta. Sosai yake ratsa duk wata gaɓa ta cikin jikinta. Ina ma dai tana da damar da za ta iya zame masa Amrah, da ta yi, ko dan ya dawo a cikin hankalinsa. A cikin ranta ta ɗauki alwashi, cewa za ta yi duk yanda za ta yi don ganin Modu ya warke, ya dawo a cikin hankalinsa. Da ikon Allah zai warke, zai koma gaban iyayensa, ƙarshen wancan mugun zai zo. How are y'all? I hope you're all fine. Sannu a hankali an fara warware ƙullallu ko in ce sarƙaƙƙun abubuwa ba? Yes! Da haka da haka za mu zo wurin. How was this chapter? Was it nice? Oh yes! Very touching😰 tausayin Modu nake. Ina matuƙar tausayawa rayuwar da soyayya ta jefa shi. Wai wasu sai su ce rashin tawakkali ne ya saka shi haukacewa? No! Ko kaɗan ba haka ba ne. Kar ku manta, soyayyar Modu (real Annur) da Amrah soyayya ce da aka gina da tubalin kirki, mai cike da tsafta. Soyayyar tsakani da Allah, wadda babu ƙarya, yaudara ko kuma ha'intar juna a cikinta. Soyayya ce wacce ta yi ƙaranci ga mutanenmu na yanzu. Ko kun manta cewa soyayya wata halitta ce, wacce Allah Yake dasawa bawa ba tare da saninsa ba? Yes! Akwai malamai da dama da ke bayyana cewa wai ma mutum ya mutu saboda soyayyar tsakani da Allah, to ya yi mutuwar shahada. Ashe dai bai kamata mu ga laifin Annur ba. Bai kamata mu alaƙanta hakan da rashin tawakkali ba.😫 Turawa suka ce; no condition is permanent. Duk yadda muke ganin halin da Modu yake ciki, akwai ranar da Allah zai kawo masa sassauci, zai kawo masa sauƙi a rayuwarsa. To ita kuma fa fiddou? Me za mu ce da ita da take mutuwar ƙaunar mahaukaci, wanda ba ta san asalinsa ba? Shin ita me ta yi kenan? Ƙauna ce kawai, kuma ta tsakani da Allah, irin wacce nake ma masu bibiyar wannan labarin, har suke kula da motsin marubuciyar, suke kiranta, da kuma tura mata saƙo a duk sanda suka ji ta shiru. Thanks all. Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:54 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 4⃣5⃣ Follow me on wattpad: PrincessAmrah Sister ɗin mai suna Sister Rita ita ta ƙudundune jinjirin da Suhaila ta haifa, kasantuwar yanayi ne na sanyi sosai, musamman kuma ga jarirai pre tamp, wanda ko kaɗan basa son sanyi. Bayan ta isar da jinjirin zuwa ga ɗakin da ake auna su, domin a zahirin gaskiya sam ba ta yarda da lafiyar yaron ba, ga wani irin numfashi da yake yi sama sama, sai fitar da nishi yake sosai. Tare suka shiga da ɗayar nurse ɗin mai suna Sister Feenah, ita kuma tana ɗauke da jinjirin da waccan shuwa ɗin ta haifa. Ɗora shi ta yi Sister Rita a bisa sikelin awo, sannan ta ce da matar wurin a yi duk abin da ya dace, za ta je ta sanar da mahaifin yaron cewa matarsa ta haihu, dan ya samu kwanciyar hankali. Bayan ta fita Sister Feenah ta miƙa ma matar jinjirin hannunta, cewa za ta koma wurin mahaifiyarsa, saboda har yanzu naƙuda take, akwai sauran jinjiri a cikinta. A cikin wannan halin ne mai karɓar dutyn rana ta iso, ba tare da Sister Rita da Sister Feenah sun dawo ba. Kasantuwar yaran dukansu ƴan ƙanana ne, yaron Suhailah ɗan ficil ne kamar an fyato, haka yaron shuwa ɗin nan ma ficil ne, kasantuwarsa twin ne. Ba lallai ba ne kallo ɗaya ka iya bambance su, kuma duk a cikin showel iri ɗaya suke, farare ne. Sister Rita ce ta dawo ɗakin, ba tare da haufin komai ba ta ɗauki yaron da ke bisa abun awon sikeli ɗin, dan ita ba ta san cewa an fitar da shi, an saka yaron shuwar ba. Bayan ta fito ta ƙariso gaban Suhaila da murmushi ta ce, "Your boy is okay now. Time da kika haife shi yana wani numfashi kamar ba shi da lafiya, and now, his breath is normal." Karɓar shi ta yi Suhaila, ta ƙura masa idanuwanta tana kallo. Fari ne sol yaron, hannuwansa duka biyun a dunƙule, kyakkyawa da shi. A cikin wannan halin suka ji zancen mutuwar wancan yaron, wanda har a lokacin wannan shuwar ba ta daina naƙudar ba. A cikin halin da take ɗin aka nemi kwali aka saka gawar yaron, ba tare da ta ga fuskar ɗanta ba, saboda wahalar da take sha, ba za a tsaya jiran har ta haihu ba, ana kallon gawar yaron haka. Ganin Suhaila ta haihu lafiya ne ya sa aka miyar da ita resting room, inda ake kai masu haihuwa bayan sun haihu, dan jiran wani lokaci, wanda a lokacin an tabbatar da lafiyarsu. Su Nadrah da Dadynsu ma ɗakin suka koma, cike suke da farin ciki da jindaɗi, Saddiqa na faɗin, "He's so cute Momy, but he's small." Suhaila ta murmusa ta ce, "Zai girma ai, ke ma ɗin da haka aka haife ki." Haka dai suka cigaba da zaman asibitin har Suhaila ta yi awa shida da haihuwa, a lokacin ne kuma aka ba su sallama, suka bar asibitin. Sister Rita ce kawai ta ga fuskar yaron da ke wurin Suhaila, ita kuma ta gama dutynta, wata ta karɓe ta. Shuwa kuma ta haifi kyakkyawan yaronta, mai kamanni ɗaya da yaron wurin Suhaila, ba su da bambanci ko kaɗan. A lokacin da Suhaila suka fito za su bar ɗakin, ita kuma Shuwa za a mayar da ita can, har suka yi kiciɓus a bakin ƙofa, Suhaila ta ɗora yaron a kafaɗarta, nannaɗe da showel. Da fara'a suka gaisa, suka ma junansu barka, ta mata ta'aziyyar jinjirinta da ya rasu, sannan Suhaila ta bi bayan maigidanta, da kuma yaranta. Haka rayuwarsu ta kasance cike da annashuwa, danginsu da ke Katsina sun zo tun saura kwana biyu suna, kowa sai yaba kyan yaron ake. Uba baƙi, uwa kuma wankan tarwaɗa, amma kuma yaronsu jajur, kamar ba Bahaushe ba. Ranar suna aka ma yaron suna da Annur, Annur Iqra Al-hussein. Ko kaɗan jikinsu bai taɓa basu cewa ba ɗansu ba ne, ba su taɓa tsammanin an musu musayar yaro ba ne. *** A cikin wannan halin da suke ciki sai ga Hadiza ta dawo, hannunta riƙe da ledar magunguna, fuskarta ƙunshe da fara'a. Tun daga nesa ta fara faɗin, "Na siyo masa duka magungunan da aka rubuta masa. Likita ya ba ni tabbaci da ƙarfin Allah ƙarshen ciwon zuciyarsa ya zo kenan. Matuƙar dai ana kiyaye ba shi wannan magungunan a kan tsari, to tabbas shi da ciwon zuciya kuma sai dai wani ɓaren, ba dai inda yake yi a yanzu ba." Miƙewa tsaye ta yi Fiddou, murmushi take mai haɗe da kuka, finally, yau dai an sayi wannan magungunan, wanda Dr. Huzaif ke goranta mata rashin siyansu. "Sannu da ƙoƙari Hadiza. Da kin sani ai ki min magana na bayar da kuɗin a siya masa, tunda akwai a wurina." Maryama ce ta yi wannan maganar bayan ta karɓi ledar, tana fiffiddo magungunan a hankali. "Babu komai ai, kuma ai ban ga kin yi canjin kuɗinki zuwa Sefa ba, ni kuma akwai su a jakata." Sai yanzu ma Maryama ta tuna fa ashe ma ba ta yi canjin kuɗi ba. To inda a ce Hadiza ba ta siyi maganin ba da ya kenan? Sai dai ta canza su inda za a karyarsu, tunda sun baro Boarder. Wani iri take ji a cikin zuciyarta. Sosai take jin ƙaunar Hadiza a ranta. Mace ce mai kirki, mai tausayi, mai matuƙar haƙuri. Sai a yanzu take jin haushin kanta na yanda take yawaita jifar Hadiza da kalamai marasa daɗi. Sam! Ba ta cancanci haka ba. Kamata ya yi ta ja ta a jikinta, cikin kalamai masu daɗi ta ringa nusar da ita illolin bariki, ta ringa kwatanta mata abubuwan da suka dace da rayuwarta. Wannan taimakon da ta ma Modu ya sa ta daɗa jin ƙaunar Hadiza a zuciyarta. Me ya sa za ta zaɓi zaman kanta a rayuwarta? Sam! Karuwanci bai kamace ta ba. Zuciyarta mai kyau ce, sosai ta yaba da karamcin Hadiza. Ba ta san sadda ruwan hawaye ya fara wanke mata fuska ba. Da sauri ta miƙe tsaye, ta rungume Hadiza, sosai Hadizar ke jin saukar ruwan hawayen Maryama a kafaɗarta. Ɗago kanta ta yi bayan ta ɗan raba jikinta da na Maryama. So take ta san dalilin da ya sa Maryamar take kuka. Tana son sanin dalilin da ya sa Maryama ta rungume ta, runguma mai nuna zallar soyayya. "Hadiza ban taɓa sanin cewa karamcinki har ya kai haka ba. Ashe haka zuciyarki take? Na yi da na sani, na yi nadamar abubuwan da na ringa yi miki a baya. Haƙiƙa na gasgata, cewa komai na duniya yana da advantage, haka kuma yana da disadvantage. Hausawa suka ce; ko kare yana da ranarsa. Kin kyauta sosai Hadiza, kin yi ceton rai matuƙa. Ladarki tana ga Allah maɗaukakin sarki, shi kaɗai zai iya biyanki wannan jihadin da kika yi Hadiza." Rungumar Maryamar ta yi ita ma tana hawayen, ta ce, "Babu komai Maryama, yi wa kai ne." Jin muryar Jiddah suka yi ta ce, "To miye abun kukan tunda dai ba wani abu ba ne? A ganina ai farin ciki ya kamata mu yi baki ɗaya, mu kuma ƙara roƙon Allah ya ba Annur lafiya." Fiddou ta ce, "Ameen hwa. Yanzu tahiya za ku yi da shi kenan?" Tana sharar ƙwallanta. Maryama ta raba jikinta da na Hadiza, ta ɗan tauni leɓonta na ƙasa, ta saka hannunta na dama ta share ƙwallar da ke malale bisa fuskarta. "Dole tafiya za mu yi da shi Fiddou. Amma kar ki zata wai Annur ya tafi ya barki kenan. Insha Allahu zai dawo gare ki, da ƙafafuwansa. Zai dawo gare ki, a cikin hankalinsa. Zai miki godiya, zai jaddada miki darajarki, martabarki da kuma begenki. Ki cire damuwa a zuciyarki, addu'a Annur ke buƙata, ita yake da muradi a wannan lokacin ba kuka ba." Duƙawa ta yi ƙasa Fiddou, daidai saitin Modu ta saki murmushi, wanda tana yinsa ruwan hawaye na zurara daga idanuwanta. Ta ce, "Annur..." Ita kanta ta ji daban, shiru ta yi ba tare da ta shirya ba, saboda yanda ta yi furucin sunan nashi, har cikin zuciyarta. "Annur tahiya za ka yi ka barni yau kam. Zan yi kewarka sosai ba kaɗan ba. Don Allah ko kaɗan ne ka ba ni gurbi a cikin zuciyarka. Ka min so ko da kaɗan ne, wanda bai kai rabi rabin wanda kake ma Amrah ba. Na maka alƙawarin jiranka, har ranar da za ka dawo bisa ƙahwahuwanka zuwa inda nake. Ina maka hwatar alheri. Allah Ya baka lahiya, Allah Ya kawo ƙarshen haukan da kake yi..." Ta yi shiru daga nan, sanadiyyar kukan da ya ci ƙarfinta. Bayan ta samu da ƙyar ta haɗiye kukanta ta ci gaba, "Allah Ya haɗa ka da Amrarka, Allah Ya sa ka same ta cikin ƙoshin lahiya." Ta duƙar da kanta a wannan karon, tana gyaɗa kanta. Sosai take kishin Amrah, kawai dauriya take. A wani ɓangaren na zuciyarta kuma tana jin wani yanayi game da Amrah, burge ta take, ko ba komai ita ɗin masoyiya ce ga masoyinta, wato mace ce da Modu ke mutuwar so, wadda da alama ya rasa hankalinsa ne saboda ita. Sosai take jin haushin kanta, na haushin Amrah da ta ringa ji na tsawon shekaru, tun daga sanda ta fara jin Modu ya ambaci sunanta. Kamata ta yi Jiddah ta miƙar tsaye. Dafe kafaɗarta ta yi cike da kulawa. Tausayinta take, sosai take jin Fiddou har cikin ranta. Cikin raunanniyar murya ta ce, "Amrah ba ta raye. Amrah ta mutu, tsawon shekaru kusan huɗu da suka gabata..." Guntse bakinta ta yi a daidai nan saboda kukan da ya zo mata, na tuno Amrah da ta yi. Tsayawa ta yi da kukanta Fiddou, ta ɗora idanuwanta da ta buɗe tsabar mamaki a fuskar Jiddah, tana neman ƙarin bayani na kalaman da suka fito daga bakin Jiddah. "Kwanan Amrah ɗaya da rasuwa Annur ya haukace. Mutuwar Amrah ce sila Fiddou, mutuwarta ce silar haukacewar Annur." Gyaɗa kanta take yi Fiddou. Ya mutuwa za ta mata haka? Me ya sa za ta ɗauki masoyiyar Annur, wacce ya fi so fiye da komai nasa? Wannan wace irin ƙauna ce Annur yake ma Amrah? Cikin kuka ta ce, "Biri yai kama da mutum..." Ta koma bakin gadon Modu, ƙirƙiro murmushi ta yi ta ce, "Ka kwantar da hankalinka Modu. Insha Allahu Amrarka tana can cikin aminci, tana zaman jiranka. Amrah taka ce, kai za ta aura, ita za ka aura a cikin Aljannah, da yardar Allah" "Yeee yeee! Na ji daɗi. Ke ma kina sonta ko? Ai na san dole ki so Amrah. Amrah ba ta da maƙiyi, duk wanda zai zauna da ita sai ya so ta. Shi ya sa ta siye min zuciya, muka yi alƙawarin aureee!" Ya ringa wasa da yatsun hannunshi, kanshi sunkuye a ƙasa ba tare da ya ɗago ba yake wannan maganar. "Ƙwarai ma kuwa. Ina son Amrah sosai, musamman ma da kake sonta. Amma ka san ina sonka ni ma?" Sai a sannan ya ɗago kansa, ya harare ta sake da baki, wani irin kallo yake mata. "Ke ni Amrah kaɗai nake so. Ai ita ta ce min kar in yaudare ta, kar in so wata macen bayan ita, kuma na mata wannan alƙawarin. So kike na zama mai cin amana? Amrah ta sha faɗa min babu kyau cin amana, ko kaɗan kar na zama mai cin amana ga kowa. Dan Allah ku kaini wurinta, ku kai ni inda Amrata take, na shaida mata ina riƙe da alƙawari, tana cikin zuciyata." Kuka sosai yake, ya dafe zuciyarsa. Sosai Fiddou ke mamakin Modu. Wani lokacin idan ya yi magana tamkar mai hankali. Duk maganar da zai yi game da Amrah ta hankali ce, babu sokana a ciki. Yana yawaita tuno abubuwan alkhairanta; nasihohin da ta ringa yi masa. Hanya ɗaya ce tal za ta yi saurin dawowar hankalin Modu, a ce Amrah na raye, ya yi tozali da ita. To matsalar wanda ya mutu ba ya dawowa. Amrah ta tafi, su da haɗuwa kuma sai a lahira. "Ka daina kuka Mod...Annur. Da kai za su tahi yanzu, za su kai ka inda Amrah." "Ka sha magani tukuna, za mu tafi ba da daɗewa ba." Maryama ta faɗa bayan ta ɓallo mishi magungunan, ta duba ƙa'idar shan kowanne, sannan ta miyar a cikin ledar, ta tura a cikin jakarta ta hannu. Robar ruwa ta ɗauko daga can bisa wata loka, ta buɗe ta, sannan ta miƙa wa Modu magungunan. "Ungo Annur, ka jefa su a baki sannan ka bi da wannan ruwan ka haɗiye." Bayan ya karɓa ya tura duka a bakinsa, ya ci gaba da tauna ko a jikinsa, kamar mai cin wani abu mai zaƙi. Gyaɗa kanta kawai ta yi, sosai take jin tausayinsa. Bayan ya taune duka ya ce mata, "Kin ga bakina, na shanye duka. Mu tafi inda Amrata." Ya wangale mata bakinsa, mai cike da zallar ƙazanta a cikinsa. Murmushi ta yi Maryama, ta ce, "Na gani to rufe bakin. Bari mu je wurin likitanka ya baka reffer, sannan mu tafi." Bai ce mata komai ba, ta juyo ga Fiddou ta ce, "Mu je wurin likitan ko?" Kama hanyar barin ɗakin suka yi, suka bar Hadiza da Jiddah a tare da Modu. A lokacin da suka isa Office ɗin Dr. Huzaif akwai patient a cikinsa, hakan ya sa suka zauna a kujerun da ke jere, na masu jiran layi ya zo kansu, na ganin likita. Ba su wani jima da zama ba patient ɗin ya fito, hakan ya sa suka roƙi alfarmar wanda zai shiga next, cewa ya musu uzuri ba jimawa za su yi a ciki ba, magana kawai za su yi. Bayan sun shiga suka zauna, Fiddou ta ɗauke kai daga dubansa, Maryama kuma cikin girmamawa ta gaishe shi. "Sannu hwa. Mun wuni lahiya?" Ya tambaye ta yana murmushi. "Alhandulillahi, Dr. Sunana Maryam, ni ƴar uwar Annur ce." "Modu?" Ya tambaye ta a daidai lokacin da yake ɗora dubansa ga Fiddou, da ke ta faman haɗe rai, ita a dole gaba take da shi. "Fiddou baby." Ya furta yana ajje wani sassanyan murmushi, mai nuna zallar tsokar da yake mata. Ba ta kalle shi ba, haka kuma ko uhm ba ta ce ba. Dama shi kanshi bai sa ran jin wani abu daga gare ta ba. "Fiddou sarkin hushi. Halan dai ba za ki huce ba haka nan? Haba mana yi murmushi Fiddou Baby. Ok ok, bar fuskar ma a haka kin hi yin kyau, sosai rashin hwara'a yake kyau a fuskar Fiddou baby." Dariya Maryama ta guntse. Wannan wane irin likita ne? Shi dai ga shi nan kamar mai tambotsai, kamar ba shi ba ne suka tarar a ɗakin ɗazu suna masifa shi da Fiddou, amma ga shi ya dage sai faman tsokanarta faɗa yake. "Fiddou baby yi haƙuri kin ji? Ɓacin rai ne hwa, amma yanzu na huce." "Kar ma dai ka huce." Ya jiyo muryar Fiddou ta faɗi haka, cikin halin ko'inkula. "Uhm...ni dai ba wannan ba Dr. I'm Annur's Sister, blood Sister." Cikin mamaki ya kalli Maryama. Blood sister? Ya maimaita a ƙasan zuciyarsa. "Wannan baiwar Allah'r da kuka tafi ɗazu har ta siya masa magani, ita ta zo wurinshi tare da Fiddou, a lokacin da ta ganshi ta gane shi, saboda an jima ana nemansa a gida har ma an gaji an haƙura, to bayan ta kai mana labarin ne muka yi waya da iyayenmu cewa ga abin da yake faruwa, Abbanmu ya ce mu ƙoƙarta zuwa mu tafi da shi." Gyaɗa kansa ya yi Dr. Huzaif. Sosai ya jiye ma Modu daɗi. Ko ba komai zai koma cikin rayuwar ƴanci, zai koma a gaban iyayensa, su kula da komai nasa. Ya tabbata za su tsaya tsayin daka wajen ganin ya samu lafiya, bakin ƙarfinsu za su nema masa lafiya. "Reffer muke so ka ba mu, don so muke mu tafi yanzu, kar mu yi dare a hanya." "Allah sarki! Amma na jiye masa daɗi sosai. Allah Ya sa hakan ya hi zama alkhairi." "Ameen Dr." Ta furta haɗe da gyara zamanta, tana sake kallon Fiddou da ke ta faman hura hanci, wai ita ta tabbatar ma Dr. Fa ba ta son raini. File ɗin Modu ya sa aka ɗauko masa, ya harhaɗa duk wani abu da ya dace, sannan ya yi short note a kan wata takarda, ya jefa ta a cikin file ɗin na Modu. "Fiddou baby halan ya za ki yi? Ko binsu za ki yi?" Banza ta masa ba tare da ta kalle shi ba. Sosai take jin haushinsa. "Fiddou baby na san hwa kina iya mutuwa idan aka tahi da giɗe. Yi haƙuri kin jiya, ke ma hwa da gangan, haka kawai ki kama son mahaukaci, wanda kika san dole ko ba daɗe ko ba jima danginsa za su zo? Idan ma danginsa ba su zo ba, bakya tsammanin duk ranar da ya dawo cikin hankali nai ya nuna bai san ki ba? Hahaha! Yi haƙuri Fiddou baby. Amrah yake so!" A wannan lokacin kam dubarsa ta yi cike da ƙuluwa. Ta kasa shanye baƙin cikin da yake guma mata. Inda a ce ya san cikin halin da take da sam bai dame ta da magana ba. Ita surutun ma duka ba ta jinsa. Ba ta jin yin masifa, amma dole ta sa ta sai ta mayar masa da martani. "Halan wai mi ruwanka da rayuwata? Ehh na ji ina son Modu, ko kana hana ni? Kuma ko abin da ya hi mutuwa zan yi ina ruwan mutum da ni?" "Babu." Ya faɗa haɗe da gwada masa tafukan hannayensa duka biyu, alamun babu ɗin. Da murmushi ya miƙawa Maryama file ɗin duka, yana faɗin, "Allah Ya ba shi lahiya giɗe." "Ameen Dr. Mun gode ƙwarai da taimakonka. Fatan alkhairi a kodayaushe." Miƙewa ta yi ta ce, "Idan kun gama kya same ni." Miƙewar ta yi ita ma Fiddou, ta buga uban tsaki haɗe da bin bayan Maryama, suka bar ɗakin. Bayan sun ƙarisa ɗakin Modu, nan Maryama ta shaida ma Jiddah da Hadiza cewa an gama komai, tafiya kawai za su yi. Raunukan da ke ƙafar Modu har yanzu ba su gama warkewa tas ba, hakan ya sa Maryama da Hadiza suka taimaka masa wurin tashi, suka saukar da shi daga bisa gadon. Fuskarsa cike take da annuri, bakinsa ya ƙi rufuwa, daɗi yake ji sosai a cikin zuciyarsa. Kallonsa ta yi Fiddou, da sauri kuma ta sunkuyar da kanta. Wani irin raɗaɗi take ji a zuciyarta. Tana jin wani sauyi a tattare da ita. Sosai duniyarta ke cike da tsantsar damuwa. Ba ta san sanda ta isa gabanshi ba, ta haɗa jikinta da nashi, duk da ƙazantar da ke tattare da shi. Rungumarsa ta yi tsam a jikinta, tamkar kar su rabu haka take ji. Bugun zuciyarsa take ji a saitin tata zuciyar, a hankali ta fara saukar da ruwan ƙwalla a bisa kafaɗarsa. Cikin taku mai sanyi Maryama ta iso gare su, gaggauta janye Fiddou ta yi daga jikin Modu. Hakan bai kasance halal ba, ba muharraminta ba ne Fiddou, dan haka bai kamata ta masa irin wannan rungumar ba. Bai ma san abin da take ba Modu, tuni hankalinsa ya kaɗu da tafiyar da za su yi. A ganinsa yau ce ranar da zai ga masoyiyarsa, wacce suka jima ba su ga juna ba. "Wata ƙila daga yau ba zan sake ganin Modu ba, wata ƙila ba zan sake saka shi a idona ba, wata ƙila ba zai sake dawowa gare ni ba. Ta yiu kallon ƙarshe nake ma Modu, sai a lahira in da rabo..." Ta saka kuka sosai, bayan ta duƙe ƙasa. "Mu je ko?" Jiddah ta faɗa tana kallon Hadiza da Maryama. Ɗaga mata kai Maryama ta yi, Fiddou ma ta miƙe duk da kukan da take, ta tattara yanata-yanata da ke ɗakin, suka fita tare, a ƙofa suka yi kiciɓus da Dr. Huzaif zai shigo, domin su yi bankwana da Modu. Gaisuwa da fatan alkhairi a gare ku. Ba zan taɓa gajiyawa da nuna muku farin cikina ba, ku ɗin nawa ne, kuna raina, ina kaunarku all fisabilillah. Wattpadians sam! Ba na jin daɗi fa. Wai sai mutum ya karanta, amma ya tsallake ɗan alamar tauraron nan ba tare da ya dangwala shi ba. Shin wani aikin wahala ne? To fa! Maryama ta sadaukar da lokacinta ɗungurugum don ganin ta taimaki Annur, ta fitar da shi daga rayuwar da yake ciki. Sosai ta hana kanta walwala da farin ciki, kawai don dawowar farin cikin Annur. Ga kuma Fiddou, wacce komanta na Annur ne. Ba ta damu da haukan da yake ciki ba, a haka take ƙaunarsa, har ba ta son rabuwa da shi. Hadiza fa? Ita kanta masoyiyarsa ce, ta ƙaunace shi, a ƙarshe ga shi ta siya masa magungunan da ake ta tsumayen samun mai siyansu. Ta zama silar samuwar wani farin ciki na daga rayuwar Annur. Ko kun san cewa zuciya ita ce jigon komai na rayuwar mutum? To Hadiza ta siya masa maganin da zai warkar da zuciyar Annur. Ya abun zai kaya? Ku juri bibiyar labarin, sannu a hankali duk za a samu mafita. Thanks all Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:55 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 4⃣6⃣ follow me on wattpad: PrincessAmrah Ba ta ko kalli inda yake ba, ta ƙoƙarta bi ta gefensa ta wuce, kasantuwar ita ce a gaba, su Maryama biye da ita. "Ba dai har kun hito za ku tahi ba." Suka ji muryar Dr. Huzaif ya faɗa, yana binsu da kallo. Da murmushi Maryama ta ce, "Wallahi fa Dr. Tafiyar kenan." "Allah sarki!" Ya furta haɗe da gyaɗa kansa yana kallon Modu. Sosai yake tausayin Modu. Hannunshi na dama ya haɗa da na Modu shi ɗin ma na dama, suka gaisa, ba tare da ya saki hannun ba ya ce, "Allah Ya baka lahiya abokina. Ina hwatar tahiyar nan ta hiye maka zama alheri hiye da nan da kake. Sai wata rana ka ji." Ya sakar masa hannun nasa, yana ƙarisa maganar da faɗin, "Allah haɗa ka da Amrarka." Sai a sannan Fiddou ta iya kallonsa, yanzu kam ba haushi ya bata ba, burge ta ya yi. Cikin dakiya da nuna jarumta ta ƙoƙarta shanye ruwan hawayenta, ta ce, "Amrah ai ba ta raye, ashe ta jima da mutuwa." Kansa ya dafe Dr. Huzaif, ya runtse idanuwansa na kusan sakan goma, sannan ya buɗe su cike da tausayi. "Lallai kuwa akwai matsala, dole ne Modu zai kamu da ciwon zuciya. Ashe shi ya sa kullum yake yawaita ambatar sunanta?" Kai ta ɗaga masa Fiddou, ba tare da ta faɗi komai ba. "Allah Ya ji kanta da rahama. Allah Ya ba Modu lahiya." Sam Fiddou ba ma ta kula da mugun kallon da Modu ke binta da shi ba. Haushinta ya ji a lokaci guda. Don me za ta ce Amrarsa ta mutu? Me ya sa za ta so raba jini da hanta? Sunkuyar da kanta ta yi ƙasa, ba ta sake haɗa ido da Modu ba, saboda har ga Allah kallon da yake mata ba ƙaramin tsorata ta yi da shi ba. Fita suka yi daga nan, suka kama hanyar barin asibitin, Jiddah da Hadiza tallabe da Modu. Sai Maryama da Fiddou biye da su a baya. Dr. Huzaif kuma ya koma Office ɗinsa. A reception suka ga Mallam Ya'u zaune yana jiransu. Yana ganin su ya miƙe yana musu sannu. Shi ya karɓi Modu ya saƙalo hannuwansa a ƙarƙashin hannun Modu na dama, ya dafo hannun Modu ɗin ya dafa a kafaɗarsa, suka ci gaba da tafiya a hankali har suka isa bakin mota. Bayan sun isa ya miƙawa Maryama makullin motar, ita ta buɗe sannan ta buɗewa Modu gidan gaba, Mallam Ya'u ya zaunar da shi, yana yi yana masa sannu. Shisshiga suka yi cikin motar, Fiddou na tsaye tana ta faman kuka, Mallam Ya'u ya tayar da mota suka bar wurin. Har suka ɓacewa ganin Fiddou ba ta daina ɗaga musu hannu ba. Wani irin ƙunci take ji a tattare da ita, wanda ita kanta ba za ta iya misalta shi ba. A nan inda take tsaye ba ta san sadda Mahmouda ya tsaya a gabanta ba. Duk ta yi nisa a duniyar tunani har ya shigo da motarsa ya faka, ya fito daga motar ya tsaya a gabanta. "Fiddou lahiya dai ko?" Ya ambata cikin wata irin murya, mai nuna zallar tashin hankali, saboda shi a tunaninshi ma ko Modu ne ya mutu, ko kuma ciwon nasa ne ya tsananta. "Sun tahi da shi, ƴan uwa nai sun zo sun tahin min da Modu." Ta duƙe a wurin tana kuka sosai, wanda duk wani mai zuciyar imani ya ji shi sai ya tausayawa mata. "To ai ba kuka za ki yi ba Fiddou. Abu ne wanda yak kamata ki ɗaga hannunki ki godewa Allah, da ya kawo miki dangin Modu, har suka tahi da shi inda suke. A gani na ai hakan zai hiyewa Modu sauƙi, zai samu kula sosai daga wurin dangi nai, wata ƙila ma ya haɗu da wannan Amrah da yake yawan hwaɗin sunanta." Kanta ta gyaɗa masa Fiddou, cikin sanyin murya ta faɗa masa cewa Amrar ma ba ta raye. Kawai dai sun yi soyayya ne sosai, wadda ita ce ma silar haukacewarsa. Ajiyar zuciya ya sauke Mahmouda, ya ce, "Ki daure to ki tashi da Allah de. Kukan naki ai babu abin da zai anhwana miki baya ga ya sakar miki wata cuta, wacce za ki rasa maganinta." Cikin sanyin jiki ta miƙe a bisa ƙafafuwanta. Sosai take jin jiri na ɗibarta, tana neman zubewa ƙasa ba tare da ta shirya ba. Komawa ta yi ta zauna a ƙasa, dafe da kanta da ke barazanar fashewa. "Daure dai ki miƙe in kai ki gida Fiddou. Dole ki ƙoƙarta rangwantawa kanki damuwar nan, Modu dai ya tahi, duk wata damuwa taki ba za ta taɓa dawo da shi ba." Ya sunkuya ƙasa ya taimaka mata, hannunta na dama ya riƙe ya miƙar da ita tsaye, bai sake ta ba har sai da suka isa gaban motarsa. Ƙoƙari yake ya buɗe mata ƙofar ta shiga, amma ina, tuni ta sulale ƙasa, ta baje wurin a sume, idanuwanta rufe. *** Satin da Annur ya cika kwana goma da haihuwa ne transfer ɗin mahaifinsa ta tabbata, inda aka miyar da shi cikin Katsina, Federal Medical Center ɗinsu. Sosai suka yi farin ciki, ko ba komai gida suka koma. Dama rabonsu da gida kusan shekara ɗaya kenan, ko zumunci ba su je ba, saboda rashin wadataccen lokaci. Yanzu kam godiya ya ma Allah, ya kuma yi fatan Allah sa can ɗin ya fi zama alkhairi a kan cikin garin Bama, saboda a wancan lokacin a Bama FMC ɗinsu take, can ne gari mafi girma, mai kwanciyar hankali a duk Borno State. A falo suke zaune, Suhaila na shayar da Annur suka ji wayar Dady ta yi ƙara. Gaggauta ɗaukar kiran ya yi, hannunsa saƙale da na Momy, wanda ta tallabo Annur ɗin da shi. Bayan sun gaisa da mai kiran nasa ya ce, "Zan shigo asibitin ai gobe kafin mu wuce, ban ma karɓarwa Annur takardar haihuwarsa ba. Ga kuma bankwana da ba mu yi ba da sauran al'umma." Ya ɗauki kusan mintuna bitu yana wayar kafin ya tsinke, ya miyar da wayar ya ajje, sannan ya dubi Suhaila cike da soyayya ya ce, "Dr. Hamdana ne, young Dr. ɗin nan da nake faɗa miki, wanda bai wuce sa'an ƙanina na uku ba." Bayan ta daidaita kwanciyar Annur da ya yi barci ta ce, "Ai yanzu kam ya wuce ƙarami, tunda ya taka matsayin da manyansa ma ba su taka ba." Tana murmushi cike da tsokana. Hannunsa ya sa ya kamo haɓarta, ya mata hararar wasa ya ce, "Babu komai dai, na ji. Ai ni ɗin ma zan zama babban Pharmacist." "Insha Allahu kuwa. Ina ma mijina fatan hakan, ya zama abun alfahari ga kowa, ga iyalinsa da dukkanin al'umma ma." Cikin tattausan lafazi ya ɗora idamuwansa bisa kyakkyawar fuskarta, ya ce, "Ina son kalar addu'ar nan taki a kodayaushe. Sosai take ƙarfafa min guiwa, nake ƙara jin ƙaunar matata na daɗa hauhawa a cikin zuciyata." Miƙewa ta yi ta ƙarisa bisa ƴar katifar Annur mai haɗe da gidan sauro, ta shimfiɗar da shi ciki sannan ta dawo ga mijinta, ta zauna ƙugu da ƙugu da shi. "Ba zan taɓa gajiyawa da yi maka addu'a ba mijina. Shin menene amfanin matar da za ta gaza buɗar bakinta ta ma maigidanta addu'a? Bata da amfani a ganina. Ta zama sokuwa, wawuya, kuma ƙatotuwar mai sakaci." A wannan karon kam sumbatar hannunta ya yi cike da bege, ya ce, "Ina alfahari da ke, zan kuma ci gaba da yin alfahari da ke har ƙarshen rayuwata, insha Allahu." Ya ɗaga kanshi ya dubi Nadrah da Saddiqa da ke tsaitsaye suna kallonsu, ba ma su san sun shigo falon ba. Da hanzari Suhaila ta gaggauta matsawa daga jikin Dady da take, saboda nauyin yaransu da ya ɗarsu a cikin zuciyarta. Ta ce, "Nadrah me ya sa bakwa sallama ne? In ce ko na sha gargaɗinku a kan ku daina shigowa wuri ba tare da kun yi sallama ba?" "Momy mun yi sallama fa, har sau biyu ba ku ji ba." Nadrah ta faɗa tana ɗan ja da baya, saboda ta san halin Momynsu, ba ta da wasa in dai wurin tarbiyya ne. Rasa abun faɗe ta yi Suhaila, hakan ya sa ta ce, "Ai da sai ku dakata daga bakin ƙofa har sai kun ji an amsa sannan ku shigo. Ina aiken da na muku?" Da tsoro ta ce, "Momy mun faɗa mata, ta ce wai to, goben kafin mu tafi za ta shigo ta kawo miki." "Good." Suhaila ta furta bayan ta murmusa kaɗan. Washe gari da sassafe suka gama shiri, motar da za ta kwasar musu kaya ma har ta tafi, da yake tun da asubah aka fara lodi. A ƙofar gida maƙofta ne da dama suka zo yi musu bankwana, har da masu kuka a cikinsu, saboda zaman arziƙi da aka yi. FMC suka fara biyawa, Pharmacy suka tasanma, Pharm IA ya yi bankwana da mutanensa, cike da jin zai yi kewarsu sosai, suka tasanma Amenity, inda za su karɓarma Annur takardar haihuwarsa. A mota ta bar su Nadrah da Dadynsu, ita kuma ta ƙarisa daga ciki, inda za a bata takardar. Bayan ta karɓa daidai za ta fita ta ci karo da wannan matar shuwa mai suna Shereefah, tafe da wata yarinya ta goyo jinjirin, wanda da alama Nanny ɗinsa ce. Da fara'a suka kalli juna, suka gaisa cike da aminci a fuskokinsu. "Ɗan yaro kana goye? Miye ne sunansa?" Shereefah Shuwa ta faɗa da murmushi. Murmushin ta sakar mata ita ma Suhailah, ta ce, "Sunansa Annur, bari na sauko miki shi." "Barshi ya yi barcinsa dan Allah. Suna mai dadi, Allah Ya raya Annur." "Ameen fa. Ya sunan na wajenki?" Karar sunan nasa take kasantuwarsa haihuwar fari, duk da kuwa ba shi ɗin ne farko ba, a tunaninta wancan ɗin da ya rasu ne farko, amma tunda dai babu shi, dole wannan ɗin za ta yi kara, tunda shi ɗin ne matsayin babba yanzu. Hakan ya sa ta kalli Nanny ɗin, alamun ta ba Suhaila amsa. "Sunansa Salman." Yarinyar ta faɗa tana fara'a. "Masha Allah! Allah Ya raya Salman. Ga shi ba su gaisa da abokinsa ba har za mu wuce." "Za ku wuce ina? Ba dai garin za ku bari ba ko?" Ta faɗa cike da zaro idanuwa tana mamaki. Suhaila ta ce, "Wallahi fa. Mu dama ƴan cirani ne, aiki ya kawo mu nan, ga shi kuma ya ɗauke mu, ya miyar da mu asalin garinmu." "Allah sarki! Allah sa hakan ne mafi alkhairi a gare ku. Amma ko sunanki ban sani ba, ga shi bani da lambarki bare a cigaba da zumunci." Introducing ɗin junansu suka yi, a ƙarshe suka yi musayar lambobin waya sannan suka rabu, ba tare da kowace ta ga yaron kowa ba. Bayan ta samu su Dady a mota ne ya ce daga nan kuma ɓangaren psychiatric za su nufa, saboda ya ma Dr. Hamdana alƙawarin za su haɗu su yi bankwana, kafin su wuce. Hakan ce kuwa ta kasance, ɓangaren da marassa hankali suke suka dosa, kai tsaye suka nufi Office ɗin Dr. Hamdana, wanda ke cike da kayan alatu, da na more rayuwa. Nadrah da Saddiqa suka gaishe shi, sannan Suhaila ma ta gaishe shi da fara'a. Dr. Hamdana mutumin kirki ne, ƙaramin yaro amma mai matuƙar girmama na gaba da shi. Shi ne the most youngest Dr. A duk asibitin, haka kuma shi ne mutum na uku da ake ji da shi a duk cikin likitocin mahaukata. Ba su wani jima ba dady ya miƙe, yana miƙewa suhaila da yaranta ma suka miƙe, Dady na faɗin, "Bari mu lallaɓa Dr. Ka san tafiyar ta mu ba ta kusa ba ce, dole sai an tafi da wuri. Na so ma a ce tun 7 mun bar nan, amma maƙota sukaita bamu shawara cewa kar mu yi fitar nan ta dugu dugu, ta cika hatsari da yawa. To motar kayanmu dai ta yi gaba, na ce da dreban yai haƙuri har gari ya waye ya nunar min da babu abin da zai faru da yardar Allah, ya tafi kawai." Dr. Hamdana ya murmusa ya ce, "Hakan ya fi ai. Allah ya kai ku lafiya ya tsare mana ku. Mr. IA please kar a yar da zumunci, a ci gaba da kula da juna, da yardar Allah ni ma ba zan taɓa mantawa da kai da ahalinka ba." Musabaha suka yi cikin aminci, Dr. Hamdana ya buɗe wata loka ya zaro kuɗi masu yawa, ya miƙawa Saddiqa yana faɗin, "'Yata ga wannan, a sha ruwa a hanya." Ƙin karɓa ta yi har sai da ya kalli Suhaila cewa ko ita ce ta hana Saddiqa karɓar kyautar da ya mata? Da fara'a ta ce da Saddiqa ta karɓa, sannan ta karɓa ɗin da godiya a bisa laɓɓanta. Har bakin mota ya raka su Dr. Hamdana, sannan ya ga sun tashi ya koma Ofishinsa. *** sai bayan magrib sannan su Maryama suka isa Katsina. Sai da suka fara biyawa suka sauke Hadiza sannan suka wuce gidan su Jiddah, ita ɗin ma aka sauke ta. A lokacin Modu ya jima da yin barcinsa, bai ma san me ke faruwa ba. Horn ɗin da Mallam Ya'u ya yi ne ya sa mai gadinsu ya gaggauta buɗe musu gate, suka shigo da motar a cikin gida. Ƙarar motar ya sa Muhammad fitowa da gusunsa, fuskarsa ƙunshe da fara'a ya tarbe su. Bayan Maryama ta fito daga motar ne ta amsa sannu da zuwan da Muhammad ke mata, ta ce, "Ka je ka ce da su Mama mun iso, kuma har da mara lafiyan, wai ina za mu kai shi?" "To." Ya faɗa haɗe da barin wurin da gudunsa, ya isa cikin falon yana faɗin, "Mama dama na faɗa miki su ne ba Abba ba. Haka Yaya Maryama ta ce wai sun zo tare da baƙo, ina za a nufa da shi?" Miƙewa ta yi Mama, ta fara ajje takunta har ta isa harabar gidan, ta inda ake faka motoci biyu da suke da su. "Barkanku da dawowa. sannu ya hanya?" Ta faɗa tana kallon Mallam Ya'u da murmushi, sannan ta ce da Maryama, "Ashe tare ɗin kuka zo." "Ehh mama, mun tabbatar ɗin shi ne fa, bari mu shiga ciki zan miki bayanin komai insha Allah." "To madalla." Ta furta bayan ta zagaya ta inda Modu yake, tana kallonsa da gyaɗa kai, tausayinsa take sosai, yanayinsa da komai nashi abun tausayi ne. Kayan jikinsa babu kyawun gani, ga wani irin zaurin fitsari da yake yi, wanda sai mutum ya kai zuciyarsa nesa zai iya haɗiyar yawu. Sosai ta yaba da ƙoƙarin su Maryama, na yadda suka taho a haka tun daga Maraɗi har Katsina. Tamkar ta zubda masa ƙwalla haka ta ji. Lallai mai rai ba wata tsiya ba ce. Duk a yadda Allah ya yi ka kawai ka gode masa, haƙiƙa ka fi wani. Duk yadda kake ganin kai mai larurin ciwo ne, ɗaga hannu ka godewa Allah, saboda akwai wanda sun fi ka larurin, wasu ga cutar ga kuma talauci da ya musu katutu, wanda ko kuɗin da za su nemawa kansu magani ba su da. Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke Mama, fuskarta ƙunshe da tausayin Modu, ta ce, "Dole inda mutane suke za a ajje shi, gudun kar ya buƙaci wani abu ba a sani ba. In baccin haka ai da sai a kai shi part ɗin can na baya, idan an gyara. Ya yanayin nasa yake? Ina nufin yana duka ko kuma attempting guduwa?" Sassauta muryarta ta yi Maryama, ta ce, "Ba ya ko ɗaya gaskiya, haukan nasa fa ba wani mai ƙamari can can ba ne, surkulle ne a kan Amrah, yai ta subbatu cewa wurinta zai je, sai idan bai samu wata maganar kirki ba ne har ya yi ƙoƙarin guduwa, cewa shi zai je da kansa ya nemo ta." Mama ta ce, "Ah to in haka ne, bida irinsu ai ba abu ne mai wahala sosai ba. Kenan dai shi ɗin ne Annur da kuke zato?" Ta ƙarisa maganar da firfito da idanuwanta, cike da mamaki. "Uhm...shi ne fa Mama. Abin da na ce zan faɗa miki kenan ai idan mun shiga ciki. Ta subbatunsa kaɗai muka tabbatar da cewa shi ne real Annur, wancan ɗin na ƙarya ne." "Subhanallahi! Lallai akwai damuwa, there's something behind, Allah kaɗai ya bar wa kanSa sani. Yanzu dai a tafi da shi ɗakin Muhammad, shi Muhammad ɗin sai ya kwana ɗakina. Kamar hakan zai yi ai." "Tunanin da na yi ni ɗin ma kenan Mama. Allah Ya taimaka, Ya ba mu ladar taimakon baki ɗaya." "Ameen Maryama. Mallam Ya'u ko za a kamo sa a shigar cikin gida?" "To ranki ya daɗe." Suka fara ƙoƙarin kama Modu, shi da Mai gadi. Cikin gidan suka shiga su Maryama, cikin yanayin gajiya ta ce, "Barin tafi sallah, ban yi ko magrib ba, ga isha na gabatowa." "To ya yi, bara na kai masa abinci, in saka Mai gadi ya taimaka ya masa wanka, zan nemo masa kaya daga cikin na Abbanku." "To Mama. Da kau ya ji daɗin jikin nasa, don da gani ya jima bai yi wanka ba. Kodayake Fiddou ta ce wai ta taɓa biyan wasu yara suka masa wanka sau ɗaya, wai yaran sukai ta masa dariya tun daga nan ba ta sake sakawa a masa wankan ba. Na tabbata zai ji sassauci a jikinsa yau. Gobe kuma sai mu saka a masa aski, gashin nan na fuskarsa duka a aske shi." Tana gama faɗin haka ta doshi ɗakinta, domin sauke farali. A lokacin da suka kai Modu ɗaki ya farka daga barcin, bin ɗakin yake da kallo sosai, yana tunanin a inda yake, saboda shi ya ma manta da inda za su je, ya manta cewa wai wurin Amrarsa za a kai shi. Ganin irin kallon da yake bin ɗakin da shi ya sa Mallam Ya'u murmusawa ya ce, "Kwantar da hankalinka, garin su Amrah ne nan, za ka ganta amma sai ka nutsu, ka yi duk abin da aka ce da kai ka yi." Bai ce komai ba sai murmushi da ya saki, miyau ya fito masa dalala, duk bisa haɓarsa. Murmushi ya yi Mallam Ya'u sannan ya fice daga ɗakin, shi kanshi yana mai tsananin jin tausayin Modu. Yana fita sai ga mai gadi ya shigo da plate ɗin abinci da cokali a ciki, ya ƙarisa gaban Modu da murmushi, yana faɗin "Na Amrah bada kanka a sare, ka je gida ka ce ya faɗi. In ba Amrah ba sai rijiya, ita kaɗai ce taka, haka kuma kai kaɗai ne nata..." Kanshi ya ringa jinjinawa Modu, alamun yana jin daɗin kirarin da mutumin ke masa. Murmushin nan bai kau daga fuskarsa ba, sai lila kansa yake, yatsunshi biyu a cikin baki, ɗaya hannunsa kuma a bisa kansa. "Abinci ne na kawo maka, idan ka ci sai na maka wanka, ka saka sababbin kaya na tarar Amrah sarauniyar mataye." Bai musa ba ko kaɗan, haka ya ringa cin abincin nan kamar wanda ya tashi daga ciwon yunwa, rabi na shiga bakinsa, rabi na sauka a ƙasa, har abincin ya ƙare. Mama da kanta ta shigo ta kawo masa kayan Abbah, masu matuƙar kyau, kuma sababbi ne sau biyu ya taɓa saka su. Bayan ta miƙa su ga Maigadi ta fita, da kanshi ya cire masa kaya, ya ɗaura masa towel ɗin da Mama ta haɗo da shi a cikin kaya, ya ɗaura masa, sannan suka nufi banɗaki. Sosai mutumin ya dirje shi, saɓi uku ya masa amma duk da haka ruwan kumfan jajur yake, tsabar datti da ya yi. A ƙarshe ya wanke masa kansa sannan ya ɗauraye shi suka fito. Wani irin sakayau yake ji a jikinsa Modu, shi kanshi yanayin da yake cikinsa ba kaɗan ɗin daɗi yake ji ba. Banda murmushi babu abin da yake saki, haƙoransa sun ɗan yi haske, saboda dirzar da suka sha. Mai ya shafa masa ko'ina na jikinsa, sannan ya feshe shi da body spray na explore, har kayansa sai da ya fesa ma turare, kafin ya saka masa su a jikinsa. Take asalin sifarsa ta fito, ya koma real Annur Iqra Al-hussei; mutum mai matuƙar kyau na fuska da na sifa, mutum mai tsantsar ƙwarjini, wanda ba kowa ke iya haɗa fuska da shi ba, tsabar ƙwarjininsa. Mutumin da murmushinsa ke haskaka kyawun fuskarsa, murmushinsa ke daɗa ƙayatar da fuskarsa. Shi kanshi mai gadi mamakinsa yake. Kyakkyawa da shi, ashe dai yanayi ne kawai ya miyar da shi a halin da yake ciki. Alwashi ya ɗauka a ranshi cewa shi da kanshi zai ci gaba da kula da Modu, zai bashi kulawa ɗari bisa ɗari har ranar da zai bar gidan, ko kuma ya samu lafiya. "To ka ga yanzu sai ka kwanta ka yi barcinka ka huta, a cikin barcin za ka ga Amrarka ta iso gare ka, ta tabbatar maka da cewa tana cikin aminci, kai kawai take jira." Bai ko jira ya gama jin maganar ba ya haye bisa gadon ɗakin, ya runtse idanuwansa yana son barci ya ɗauke sa. Murmushi kawai mai gadi ya yi, ya kashe masa wutar ɗakin sannan ya jawo ƙofar, yana mai matuƙar jin tausayin Modu, tunda Mama ta masa bayani kafin ya shigo yi masa wanka. Tun bayan ta yi sallah ta yi wanka ta fito falon, ta tarar Mama ta zubo mata abinci, ta haɗa mata komai tana jiran ta je ta ci. Zama ta yi a ƙasa ta jawo abincin kusa da ita, ta jiyo muryar Muhamnad na faɗin, "Yaya Maryama ya bani taisayi sosai. Ina jinsa yana faɗin Amrah, hala dai wacece Amrah?" Murmushi ta yi Maryama, ta ce, "Masoyiyarsa ce." Kawai ta yi shiru haɗe da fara kai lomar abinci a bakinta. Sai da ta yi nisa ma ta tuno da wani abu, ta ce, "Mama na tuna, Annur fa an hana ba shi duk wani abinci mai cholesterol a cikinsa." Da fara'a Mama ta ce, "Na sani, duk wani mai larurin zuciya akan hana ba shi choleterol, shi ya sa na yi wannan tunanin, na tura aka siyo min non cholestetol oil, da shi na yi girkin." Ajiyar zuciya ta sauke Maryama ta ce, "Yauwa. Sai kuma abu ɗaya, bai sha maganinsa na dare ba." "Subhanallahi! Kuma da ƙyar idan ba ya kwanta ba. Tashi mu je mu ga, Allah sai bai yi barci ba." Tashin kuwa suka yi a tare har da Hammad, suka isa ɗakin da ke ɗan nesa da na Abbah. Kunna wutar ɗakin suka yi, yanayinsa kawai ya saka su murmusawa su duka ukun. Kwance yake idonsa a rufe, sai ƙyaƙƙyaftu yake, wanda kallo ɗaya za ka masa ka tabbatar cewa ba barci yake ba. Cikin murya mu ƙunshe dariya ta ce, "Angon Amrah tashi ka sha maganinka, sannan ko koma barcin." Firgigit ya buɗe idonsa, yana sakin murmushin yaƙe ya miƙe zaune. Deep freezer ta buɗe ta ɗauko ruwan Sona guda ɗaya, sannan ta buɗe, ta ɓallo masa magungunansa da ke can bisa side drawer ta ba shi. Sai da suka tabbatar ya sha sannan suka bar ɗakin, bayan sun kashe masa wuta. *** How are y'll? Fatan muna lafiya. Ya iyali ya shirye shiryen sallah? Allah sa komai lafiya. Ya kuka ji wannan shafin? A yanzu dai na tabbata na warware nuku kawuna, dangane da Annur da kuma Sans. Na tabbata akwai da dama masu cewa kawunansu na a duhu, wai ba su gane komai a kan salon namu na yanzu, na kwan gaba kwan baya. Kafin mu fara dama na shaida muku cewa za mu canza salon labarin, mu taɓo farko sannan kuma mu taɓo ci gaba, tun daga yanzu har a gama warware mana silar zuwan real Annur Maraɗi, da kuma silar dawowar fake Annur (Sans) gidan su real Annur. Fatan za ku ci gaba da bibiyata, har izuwa wannan lokacin. Masu faɗin wai marubuciya Amrah ba ta kyauta ba, me ya sa za ta ce Annur Iqra Al-hussein wai ba ainahin ɗan Pharm IA ba ne? Ku ajje hankulanku ku fahimci labarin nan, za ku ga kamar ya sha bamban da dama labarukan da kuke karantawa. Salo ne a cikinsa da ba koyaushe ake amfani da irinsa ba. Ku duba tun daga jigon labarin; aure da ake yi ba tare da awon genotype ba, shin ana yawaita taɓo ire iren jigon nan kuwa? Da wuya kam. Saboda haka a yi haƙiri dai, a kuma ƙara yin haƙuri, sannu a hankali duk za mu kai ga inda za ku buɗe baki, ku yi dariya sosai tsabar farin ciki. Ina ma kaf al'umnar musulmai happy sallah in advance. Allah Ya sa mu yi sallah lafiya. Sannan ƙarin tunatarwa, a bi a hankali wurin cin nama, dan kar a ci aita zawo😂 ahto, kar ku ce Amrah ba ta faɗa muku ba. And a ajje min nawa naman, duk wacce ba ta ajje min ba za mu ɓata, kuma sai after one week zan ringa muku posting...lol😜 Sai kuma bayan sallah idan Rabbussamawati wal-ard ya nuna mana sannan za mu sake haɗuwa. Mu dage da ibada a cikin ƴan kwanakin nan da suka rage kafin arfah, Allah Ya karɓa mana ibadunmu ameen. 4k words na muku kawai don farin cikin zuwan sallah. Fatan kun yi enjoying reading na shi. Thanks all Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:55 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 4⃣7⃣ Taƙabbalallahu minna wa minkum. Fatan mun sallata lafiya. Allah ya maimaita mana amin. Wanda suka yi aikin Hajj Allah sa sun yi karɓaɓɓe. Wanda suka azumci ranar arfah, Allah ya karɓa, ya gafarta mana kurakuranmu ameen. *** Haka Annur ya ci gaba da rayuwa a gidan su Maryama, ba tare da wata matsala ko kaɗan ba. Sosai suke ba shi kula, tamkar jininsu ne shi. Yadda suke tarairayarsa ko a gidansu yake iyakacin abin da za a masa kenan. Sai dai a kowace rana ƙaranci ya kira sunan Amrah sau bakwai. Amrah yake so, a kai shi wurin Amrah, ya san ita ɗin ma tana can tana jiransa. Kalaman da yake yawaita furtawa kenan, yayin da ruwan hawaye kan kwaranya daga ƙwayar idonsa zuwa bisa fuskarsa, a duk sadda zai neme ta. Maganinsa kam babu tangarɗa haka yake shansa, da zarar lokacin sha ya yi Mama za ta ce da Maryama ta je ta ba shi. Haka abincin da yake ci duk an bi ƙa'idarsa, baki ɗaya suka daina amfani da normal oil a gidan, sai dai non cholesterol, kurum don inganta lafiyar Modu. Yanzu haka kwanakin Modu biyu kenan a gidan su Maryama, amma yadda suka shaƙu sai mutum ya ce sun shekara guda a tare ne. Sosai ta iya tafi da mahaukaci, kasantuwarta psychologist ce, psychology take karanta. Kusan duk irin wannan abubuwan ba baƙinta ba ne, ta san hanyar sarrafa shi sosai. Hatta makarantarta ta sahale da zuwa, babban burinta kawai ta shawo kan matsalar Modu, saboda ta fuskanci yana buƙatar wadataccen lokaci, yana buƙatar mai tausar zuciyarsa, haka kuma yana da buƙatuwar mutum mai muhimmanci a tattare da shi. Wannan dalilin ne ya sa ta sadaukar da lokacinta gare shi, take son zama mai muhimmanci a rayuwarsa, ta yadda burinta zai yi saurin cika. A islamiyya ma da yake sun gama rehearzal, yanzu jiran ranar yi kawai ake, nan da kwanaki huɗu za a yi ta. Babban burin Maryama shi ne ta kammala da abin da ke gabanta; wannan walimar saukar, sannan ta hau bincikar inda za ta samu babban likitan ƙwaƙwalwa, wanda zai duba Modu, ya kuma sama masa lafiya da ƙarfin mulkin Allah. Zaune take da waya a hannunta, browsing take, sosai take bincikar matsalar Modu. Tun daga farkon damuwarsa, har izuwa haukansa, da kuma ciwon zuciyar da ya samu ta rubuta, tana mai neman shawara, tana son sanin haƙiƙanin abin da ya kamata ta fara bi, wurin tabbatar da lafiyarsa. Shawarwari ta samu kala daban daban, wanda duk wadda ta ɗauka, sosai za ta iya zame mata mafita. Sai dai kuma inda matsalar take, ita ɗin ba ta kasance wacce ya san ta tun asalinsa kafin ya haukace ba. A mafi rinjayen shawarwarin kuma, sun ginu ne a kan ta nemi wanda ya sani kafin haukansa, wata ƙila zai iya tuna wani abu, har memory ɗinsa ya dawo daidai. Mafi ƙaranci daga cikin shawarwarin, sun nunar mata da cewa wai ba hauka ba ne Modu yake, kawai dai ya yi losing memory ɗinsa ne. Don haka kawai ta ci gaba da zama a haka, ta yi haƙuri, a kowanne lokacin memory ɗinsa zai iya dawowa daidai, zai iya tuna komai da ya faru a baya. "How could this happen? Ban gasgata wannan ba. Idan har losing memory ɗinsa ya yi, ai ba zai riƙe suna guda a rayuwarsa ba. Ba zai riƙe sunan Amrah, wacce ta kasance mai muhimmanci a gare shi ba. Da sai ya manta har ita ɗin, babu wanda zai zauna a ƙwalwarsa." Ta faɗa a bayyane, tana mai rubuta comment a ƙasan wannan maganar, cike da al'ajabi. Bayan ta rubuta wata mace mai suna Sandra ta sake rubuto mata; hakan ba abun mamaki ba ne. Ai don an ce mutum ya yi losing memory nashi, ba lallai komai ne zai fice masa a ka ba. Akwai abubuwan da ka iya zaunawa zaman daram a kwanyarsa, musamman ma Amrah da ta faɗi kalar darajarta a gare shi. Sosai tashin hankali kan kawo matsalar losing memory; ta yiu wata mummunar kalma ce mutum ya ji, wani tashin hankali ne ya gani, duk sukan iya ruɗa mutum, ya fita hayyacinsa, har ya manta komai na shi, sai dai kuma za ta iya yiuwa ya riƙe wancan abun wanda ya ji, ko kuma ya gani, har ya yi silar mantau ɗin. Shawarar da take ba ta, ta ci gaba da kula da shi, ta ci gaba da kyautata masa, tana bin duk wata maganarsa. A duk sadda zai furta Amrah yake so, ta ringa ƙarfafa masa guiwa, ta tabbatar ba ya yawaita shiga ƙunci. Kukan nan da yake, ta san duk yadda za ta yi wurin faranta masa, har ya mance da ɓacin ran da yake ciki. Ta kasance mai yi masa labaran soyayya, tunda dai ta silar soyayya ya shiga ƙuncin, da har ya miyar da shi haka. Ta nuna mishi ƙauna sosai, ta ba shi kulawa, har lokacin da za ta zama mai muhimmanci a gare shi, tamkar Amrar da ta yi silar komai na shi. Murmushi Maryama ta yi a daidai wannan lokacin. Ta jinjina kanta alamun gamsuwa, ta ɗan lumshe idanuwanta sosai tana jinjina lamarin. Sosai ta yarda da hakan. Sai dai fa mafi rinjaye na zuciyarta, ya fi yarda ne da cewa lallai hauka ne yake yi, tana da wata tambayar. A ƙasan comment ɗin Sandra ta sake rubuta; na gamsu sosai da bayananki, amma kuma idan har losing memory ne ya yi, ai kamar ba zai ci gaba da yin abubuwa irin na taɓaɓɓi ba. Da hankalinsa, kawai dai ya manta komai na shi ne, sai Amrah kawai. Alamun murmushi Sandra ta turo mata, ta ce babu abin da losing memory ba ya haifarwa. Zai iya zautar da mutum ma, koda ba mahaukacin ba ne, a ga ya zam tamkar mahaukacin. Kar ta taɓa tunanin hauka ke damunshi, domin yana da wuya irin haka ya haukatar da mutum, sai idan wani mummunan hatsari ya samu kansa ya bugu har ya taɓo sashen ƙwalwarsa, wanda zai gaggauta harbar wani sashe na daga cikinta da zai tsayar da duk wata hanyar da za ta yi ordering mutum abu. Kenan komai mutum zai yi zai koma disorderly. Abu na biyu kuma idan ya kasance kafin mutuwar Amrah, shi ɗin drug abuser ne, a hankali kwanyarsa ta fara taɓuwa, sai kuma aka yi katari da case na mutuwar ya iso, a take komai zai iya jagulewa, ya haukace kenan. Mafi zargi dai losing memory ɗinsa ne kawai ya yi, amma mai tsananin gaske, mai haɗe da juyewar hankali kaɗan. Ɗan taunar leɓonta ta yi Maryama. Sosai take mamakin kalaman Sandra. To amma, alzheimer's disease (Ciwon mantau) ta kama shi kenan? Sake rubuta ma Sandra ta yi; tun daga mutuwar Amrah kenan alzheimer's disease ta kama shi? Sandra ta ce ko kaɗan ba zai yiu a ce alzhermer's disease ba ce ta kama shi. Saboda ita alzhermers fa komai mutum mantawa yake, including his language. Ya koma tamkar ɗan koyo, komai sai an koya masa. Kuma abun haushi da zarar an koya masa zai manta. Akwai wanda na shi ke iya ɗaukar tsawon awoyi kafin ya manta ɗin, akwai kuma wanda a take za a koya masa, kuma a take zai manta. Shi kuma wannan har sunan Amrah yake faɗi, ya iya yarensa sosai. Ba za a taɓa alaƙanta shi da mai alzheimer's disease ba. Godiya sosai Maryama ta ma Sandra, sannan a ƙarshe ta tambaye ta ko ta san wani likita wanda yake da wannan ilimin sosai ta haɗa ta da shi? Sandra ta ce ita kanta ɓangarenta kenan, sai dai kuma ba a Nigeria take ba yanzu, UK take. Idan har za su iya kawo shi nan ɗin, babu damuwa, she can help them. Maryama ta ce ko a cikin abokan aikinta ba ta san wani da ke Nigeria ba? Ta ce mutum biyu ta sani sosai da wannan ilimin; Dr. Aqaaq Saifullah, sai kuma Dr. Hamdan M Ramat, wanda ya kasance mentor ɗinta. Za ta nemi amincewarsu idan sun yi waya, ko me kenan, tai dropping digits ɗinta, she will contact her. *** Tun daga sadda rayuwar su Suhaila ta dawo Katsina Pharm IA ya koma karatunsa, a Sudan. Da haka rayuwarsa yaran nasa ta fara ginuwa a bisa turbar kirki, Nadrah da Saddiqa sun shiga wata makaranta mai kyau, domin samun ingantaccen ilimi kamar yadda mahaifinsu yake so. A tsawon wannan lokacin sosai Annur ya fara yin wayo, dariya yake sosai duk da cewa watansa biyar kenan da ƴan kwanaki duniya. Kyakkyawan yaro ne jajur da shi. Idanuwansa farare ne sol, masu matsakaicin girma. Jikinsa ɓul-ɓul irin wanda kowa ke da muradin ɗaukar irinsu. Sumar kansa kwance take luf-luf, wacce idan yau aka aske ta, gobe za a fara ganin alamun tsirowarta. Bakinsa ɗan ƙarami ne, da siririn hanci, wanda kumatu ya cinye fiye da rabinsa. Komai na yaron abun birgewa ne. Ga uwa uba kuma fara'ar da gare sa, wadda kan jawo hankalin mutane a kodayaushe. Kwanaki na tafiya, awanni na tserayya, mintuttuka na gudanya, sakan na kwararar gudu, har Pharm IA ya cika shekara huɗu a Sudan, inda ya kammalo karatunsa, ya zama babban pharmacist, wanda irinsu ke wuyar samu a ƙasarmu ta Najeriya. Bayan ya dawo ƙasarsa ne kuma aka saka Annur makaranta ta boko da ta islamiyya. Watansa huɗu da dawowa kuma Suhaila ta samu wani cikin, wanda ta haifi kyakkyawar yarinyarta, sai dai ita ɗin baƙa ce, kamar sauran danginta mata. Jameela sunanta; sunan kakarta aka saka mata, mahaifiyarta ta mata laƙabi da Islam, saboda tsananin son sunan da take. A cikin lokutan da Annur ya fara mallakar hankalin kansa ne Allah ya jeho Amrah a rayuwarsa, sanadiyyar wani dalili da ya sa mahaifiyarta ta zo ƙofar gidan su Annur ɗin, har ya ga Amrah, a lokaci ɗaya ya kamu da begenta, duk da kasantuwarsa ƙaramin yaro. Ya ɗauke ta ya ajje a cikin zuciyarsa. Ya sadaukar da komai nasa saboda Amrah. Duk inda zai je sai ya biya ta gidan su Amrah ya ganta sannan yake samun kwnaciyar hankali. Haka ita ma Amrah, tun tana ƴar ƙaramarta ta shaƙu da shi, ta saka shi a cikin zuciyarta, izuwa lokacin da aka raba su, aka miyar da shi Cyprus wurin yayarsa Nadrah. A ɓangaren Salman ma dai haka ya ringa yin wayo, kyakkyawa da shi wanda ko kaɗan ba shi da bambanci ko kaɗan da Annur, kamarsu ɗaya, komai nasu ɗaya. Sai dai matsalar babu wanda ya sani, babu kuma wanda zai iya fayyace musu gaskiya sai Dr. Rita, saboda ita kaɗai ta san kamannin Annur, ta kuma san cewa shi ne a hannun Suhaila. Matuƙar za ta ga hoton Salman na jarintaka, to tabbas za ta tabbatar da cewa kamanninsu iri ɗaya ne da Annur. *** Tunda suka zauna a gaban teburin likitan gabansu ke tsananta faɗuwa, barinma Farouk Sardauna da hankalinshi ya gama tashi, jikinshi ya gama ba shi cewa lokacin mutuwarsa ya kusa. Suna cikin haka sai ga likita ya shigo sanye da lab court, idonsa sanye da medical glasses yana faɗin, "Afwan na barku da jira. Abokin nawa sai da na kai shi har gaban mota ne." "Babu komai." Annur ya furta haɗe da ƙirƙiro murnushi yana bin Dr. ɗin da kallo. Bayan ya zauna a mazauninsa ya zare glasses ɗinsa, ya sauke nannauyar ajiyar zuciya, sannan ya hau duba results ɗin Bobby. Sosai Bobby ke jin raɗaɗi a zuciyarsa, yake jin duniyarsa na sauya masa, tashin hankali wanda tunda yake a rayuwarsa bai taɓa yin irinsa ba yake ji. Firgigit ya zabura haɗe da dawowa hayyacinsa, a lokacin da ya ji tattausan kalaman likitan, ya ƙura masa idanuwa, "Ya kake da wannan bawan Allah'n? Ina nufin can I say anything infront of him?" Da kai Bobby ya ba likita amsa, cewa ya faɗa ɗin kawai. A wannan lokacin kam ya gama sadaƙewa, ya kuma tabbatar da cewa ba ƙaramin ciwo ba ne a tattare da shi, tunda har likitan ba ya son faɗi a gaban Annur. "A bisa hotuna da aka maka ga su, sun bada tabbacin cewa hunhunka ne ke da matsala. Shi ne ya yi damaged, gurɓatarsa har ta fi lafiyarsa yawa. Ko ka san abin da ya jawo haka kuwa?" Ya sake gyara zamansa, har yanzu bai ɗauke idonsa daga fuskar Bobby ba. Bai jira amsar da Bobby ɗin zai ba shi ba, ya ɗora da faɗin, "Smoking ne, shi ne sila Farouk!" Ido buɗe Bobby ke sake dubar Dr. Ba tare da ya furta komai ba yake zubar da ruwan hawaye, yana ɗan gyaɗa kansa. Annur ɗin ma bai iya faɗar komai ba, sai dai fa cike yake da tausayin amininsa, sosai yake jinshi har cikin zuciyarsa. Me ya sa ciwo zai musu haka? "A duk sadda mutum yake shaƙar hayaƙi, ko kun san cewa wannan da kuke tutiyar ai kuna fiddo shi ta baki da hanci, ba dukansa yake fitowa ba? Sannan kuma dole sai ya isa cikin hunhunku, sannan ma duk abin da zai yi ya yi? Wannan smoking ɗin da kuke ji da gani, ba shi da wani amfani a gare ku face matsala, wadda za ta iya kai mutum ƙabari. Yanzu dai ga shi, baki ɗaya hunhunka ya yi damaged, sauran amfaninsa kaɗan ne, matuƙar ba a tashi maka tsaye ba, akwai babbar damuwa. Abun haushi, har da wata sabuwar sigari aka kawo yanzu, wai ita shisa. Kun san cewa duk illar da sigari za ta yi ita ɗin ma za ta yi shi? Yes! Za ta yi shi. Saboda hayaƙi ce ita ma, an shaƙe ta ne kuma aka isar da ita cikin ciki, kuma kai tsaye hunhu za ta kai mawa. Shi hunhu wani irin abu ne, wanda babu wuya yake shafewa. Yanzu ku ɗauki misali, a nemi hunhun rago a yanka shi manya manya, sai a tsoma shi cikin ruwan mai, wuta ta bige shi. Ya zai yi? Zai koma ya laƙume, tamkar ba manyan yanka aka yanka shi ba. To haka ko na mutum ma yake yi, da zarar ana kai masa hayaƙi, wannan laƙumewar haka zai yi ta, a hankali har ya kai minzalin da zai gama lalacewa. Ko mata masu amfani da icce wurin girki, ana yawaita faɗakarwa a kan hakan, cewa su daina zama a bakin wutar sosai, matuƙar suka haɗu da icce mai hayaƙi. Saboda wannan hayaƙin zai iya yi musu illa, sosai zai harbi hunhunsu. Su ɗin ma da ya zamewa dole kenan. Amma ku sai ga shi kuna kai kanku halaka da kanku. Kuna yin abin da ba zai amfane ku da komai ba. Ba za ku ƙaru da komai ba face ciwo mai girma. Why? Me ya sa kuke haka?" Ya dakata daga nan, yana mai tsananin jin takaicin Farouk Sardauna. A wani ɓangaren na zuciyarsa kuwa, tausayinsa yake, ta yadda yake yaro matashi, amma wannan cutar ta kama shi, wacce ba lallai ma ya ci gaba da rayuwa ba. Dafe kansa ya yi Dr. Da ƙyar ya iya ci gaba da faɗin, "Akwai drugs da zan rubuta maka, a dage amfani da su, bayan sati biyu sai ka sake dawowa." Godiya Annur ya masa, zuciyarsa cike da rauni. Tausayin abokinsa ya gama mamaye duk wata gaɓa ta cikin zuciyarsa. Ƙwaƙwalwarsa yake ji tana juya masa, tana neman dagula duk wani lissafi nashi. Bayan Dr. Ya rubuta musu maganin ne suka miƙe, jiki ba ƙwari suka bar Office ɗin na shi. *** My pipu how are y'all? I hope na same ku lapia😍 its been a while ba mu hadu ba ko? Tun kafin sallah. Hidimomi ne suka sha gabana, kun san sallah akwai dadi, zumunci ake sadawa sosai😀 yanzun ma fa kar ku zata an gama. Masoya ANS ne kawai suka taso Amrah a gaba,🤒 don dole na na kokarta taipa muku wannan, ba wani mai yawa sosai ba🤦 To ya kuke gani fans? Waye ne Dr. Hamdan M. Ramat din nan, wanda Dr. Sandra ta ce mento dinta ne? Kamar dai farkon haukar Annur ai Dr. Aqaaq Saifullah ya duba shi ba a dace ba.🤔 Bayanan da Dr. Sandra ta ma Maryama hakan zai iya kasancewa ko ba zai iya ba? Ina za mu iya gano Sister Rita bare ta warware mana wannan kullalliyar, mai wiyar kwancewa? Me kuka hasaso ne a wannan ciwon da Farouk Sardauna (Bobby) yake yi? Kar fa ya mutu, ina kaunar Bobby nawa🤧😱 A tabbatar an dropping comments, kafin zuwan next chapter. Vote, comment and share with your family and friends. Thanks all Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:56 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 4⃣8⃣ Wattpad me: PrincessAmrah *** Tun bayan shigarsu mota Bobby ke kuka sosai tamkar ƙaramin yaron da ba ya jin rarrashi. Yana yin kukan yana wani irin tari, wanda da zarar ya tara hannunsa ya fiddo kaki sai ya ga gullamar jini ce. Hakan ba ƙaramin ƙara tayar da hankalin Annur ya yi ba. Ya ma kasa rarrasarshi, shi kanshi ji yake ina ma dai ruwan hawayen ya zo, da bai ga abin da zai hana shi barinsa wanzuwa a saman fuskarsa ba. Da ƙyar ya iya rintse idanuwansa Annur, ya buɗe su da wani guntun ƙwalla, mai matuƙar zafi a gare shi. Cikin nutsuwa da kwantar da kai ya fara ajje kalamansa, zuciyarsa na ƙuna sosai. "Ka yi haƙuri Guy, ka kai zuciyarka nesa. Kar ka zata wai don kana cuta hakan na nufin ka kusa mutuwa ne, ko kaɗan ba haka ba ne. Cuta ba mutuwa ba ce..." Yana neman ci gaba da magana Farouk ya dakatar da shi, cikin sassarfar murya, bakinsa na rawa sosai ya ce, "Kar ka damu guy. Ka kwantar da hankalinka, na ga ka tasarshi sosai kawai don ba ni da lafiya. Idan ma mutuwar ce ina da maganinta ne?" Ya saki guntun murmushi, wanda za a iya kiransa da na yaƙe, ya ci gaba, "Abokina hunhuna fa ne ya lalace, kana sa ran zan ci gaba da rayuwa ne? Na cire rai da rayuwa guy. Ka kai ni gida please!" Babu musu Annur ya ja motar tashi, suka bar harabar asibitin. Ko a mota babu mai cewa kowa uffan, sai saukar ajiyar zuciya kawai da ke fita. Abun mamaki, su ɗin da suka kasance masu ƙure sautin mota, sai ga shi yau babu. Su ɗin da suka kasance ba a raba su da kayan maye a cikin mota, yau babu. Su ɗin da suka kasance masu raha da shewa a cikin mota, yau babu ko ɗaya. Lallai wannan rayuwar abun tsoro ce. Kana taka Allah na naSa. Kana nan sake da baki kana bankaura, ba ka san ya rayuwarka za ta kasance ba. A duk inda rayuwar ɗan maye take, ba ta taɓa tasiri a ƙarshe, ba zai taɓa aikata abun kirki ba a ƙarshe, matuƙar bai shiryu ba. A haka suka isa gidan su Farouk ɗin, bayan ya kashe motar ya zagayo ya taimaka masa ya fito, tafiyar kanta a wahalace yake yin ta, saboda cin ƙarfinsa da tarin ya yi. Kuma idan ana kuka dama tari ya fi ta'azzara. Har ɗakinsa ya kai shi sannan ya kunna masa AC, saboda zufar da yake yi. A zuciyarsa Annur yake tunanin yadda rayuwa ta juyewa abokinsa a tashi guda. Dafe kansa kawai ya yi, yana ƙoƙarin shanye kukan da ke niyyar kufce masa. *** Cike yake da mutane gidan na su, sai shige da fice ake, ana ta shirye shiryen tafiya wurin walima. Tun bayan da ta yi wanka sam hankalinta ba ya jikinta, yana ga Modu da take tunanin za ta fita ta bar shi yau. Ga shi kuma idan ta tafi wurin walimar, ba da an gama za ta dawo gida ba. Sai sun yi tasu ta musamman a tsakanin ƴan ajinsu. Tagumi ta rafka, ta rasa uwar ubanta. Ji take kamar ta ɗaura hannu a ka ta yi kuka, sai dai babu dama. A wani sashe na zuciyarta kuwa ji take ina ma a ce an ɗaga wannan walimar, har zuwa wani lokaci, duk kuwa da zakwaɗin zuwanta da ta ringa yi a baya. Sallamar Muhammad ce ta dawo da ita daga duniyar da ta lula ta tunani. Saurin amsa sallamar ta yi haɗe da ci gaba da shafa powder, tana ƙoƙarin miyar da komai ba komai ba. "Yaya Maryama, Mama ta ce wai ba ki gama shiryawa ba? Wai kar a makara. Kuma kar ki manta da maganin Yaya." "Na kusa kammalawa Hammad. Ka ce ina zuwa. Na ba shi maganin tun kafin na yi wanka." Ficewa ya yi a guje tare da sanarwa Mama saƙon Maryama. Jiki babu ƙwari ta gama kimtsawa. Hijabinta ta zira har ƙasa sannan ta fito, mutane ta gani dangin Mama da na Abba, zazzaune da yawa, wai a haka ma wasu sun yi gaba tare da Abbah, wasu kuma Mallam Ya'u ya tafi da su, sai ya dawo ya ɗauki Maryama sannan a kwashe sauran mutanen. Har ƙasa ta duƙa ta gaggaishe su, sannan ta nufi ɗakin Hammad inda Modu yake, ta same shi zaune ya yi tagumi, ruwan hawaye na kwaranya a bisa fuskarsa. Yana ganinta ya yi gaggawar janye hannuwansa daga tagumin da ya yi, saboda ta ce da shi matuƙar bai daina yin tagumi da kuka ba, ba za ta taɓa kai shi inda Amrah ba. Wannan dalilin ne ya sa duk sadda za ta shigo zai kwantar da hankalinsa, ta ci gaba da saka shi cikin farin ciki da walwala. "Ba ka daina ba ko?" Ta faɗa tana harararsa, bayan ta ƙarisa shigowa cikin ɗakin. Kansa ya ringa gyaɗa mata, yana ƙoƙarin yin dariyar yaƙe, wanda a kodayaushe ya yi shi, sai zuciyar Maryama ta sake karaya, saboda ji take ina ma dai ya dauwama a haka cikin walwala, ina ma a ce hankalinsa ya dawo gangar jikinsa. "Yauwa ɗan albarka. Yau ba za mu samu damar yin wannan darasin ba. Amma dai ina fatar ka haddace wancan ɗin da muka yi." Kansa ya gyaɗa har yanzu bai daina mata murmushi ba. "To ɗan tuna min ma, a ina muka tsaya?" Ta karkaɗe kunnenta haɗe da nuna masa shi da hannunta. Toshe bakinsa ya yi sannan ya fara magana ƙasa-ƙasa, wacce duk kusancinka da shi ba za ka taɓa gane me ya faɗa ba. "Ya Noor ba na jin ka fa." Ta faɗa da wata murya, tana kallon cikin idanuwansa. Baza mata na shi idanuwan ya yi yana kallo, haka kawai ya samu kansa cikin bege, ya ƙara tuno wasu abubuwa game da Amrarsa. Shiru ya yi, gabansa na tsananta duka, ya kasa koda ƙyafta idonsa ne. Ganin haka ya sa Maryama ta raina kanta. Ta rasa gano manufarsa, ta kuma samu kanta da faɗuwar gaba. "Uhm...bara na tafi." Janye hannuwansa ya yi daga bakinsa, ya ɗan langaɓe kansa, da murmushi ya ce, "Kin ce wai soyayya da ƙauna suna da bambanci. Soyayya takan ƙare a wasu lokuta, saɓanin ƙauna da babu abin da ke kankare ta. Kuma kika ce...me ma?" Ya ɗora hannuwansa a kumatu alamun tunani. Sannan ya murmusa ya ce, "Wai akan yanke soyayya ta wani dalili. Ko mutum ya naƙasa, ko ya haukace, idan soyayya ce ake yi to za ta gushe. Ita kuma ƙauna duk wuya duk rintsi ana tare. Babu abin da ke lalata ta. Kuma a ƙarshe kika ce wai irinta ce nake ma Amrahhhh." Ya ja maganar a ƙarshe, haɗe da rufe idanuwansa alamun kunya. Tafa masa ta yi tana dariya. "Good job Ya Noor ɗina. Lallai kana ganewa sosai, kwanyarka tana ja. Na tabbatar kam ka fahimci wannan darasin, sai kuma gobe insha Allahu za a ƙara maka wani." Ɓata fuskarsa ya yi alamun jin haushi, "Ni yau nake so." Samun wuri ta yi ta zauna a kusa da shi, ta sauke ajiyar zuciya haɗe da faɗin, "Ka cika rigima Ya Noor. Yau fita zan yi fa. Ranar farin ciki ce a gare ni, kai ma ya kamata ka zama a cikin farin ciki. Walimar saukarmu fa ake yi." Zullo ya hau yi a saman gadon, yana jin daɗi sosai ya ce, "Amrata ma an musu walimarsu ta sauka." Dafe kanta ta yi Maryama, nan ta fara tunowa da kalaman Sandra, inda ta tabbatar mata da cewa losing memory ɗinsa ne ya yi Annur. Kuma dama mutum yakan tuna wasu abubuwa da suka danganci dalilinsa na yin losing memory ɗin. Wanda idan har zai samu mai ɗora shi a saman hanya, sannu a hankali zai fara dawowa hayyacinsa. Zai fara tuna komai na rayuwarsa da ya manta. "Zan tafi. Anjima Hammad zai zo ya ba ka maganin rana. Kar ka musa masa, da zarar ya ba ka ka karɓa ka sha, idan ba haka ba kuma zai faɗa min, kuma ba za mu sake yin darasi ba." Kai kawai ya gyaɗa mata, da haka ta fice daga ɗakin, ta samu har Mallam Ya'u ya dawo, wucewa kawai suka yi zuwa Islamiyyarsu. * Taro ne na ji da faɗa aka yi. Rumfuna aka kafa manya manya, ga plastic chairs nan birjik an jera. Ga ɓangaren da manyan baƙi za su zauna, da kuma na sauran al'umma. Sai daga can gefe kuma masu saukar ne sai farin ciki suke. Maryama da Jiddah jere suke da juna, komai nasu iri ɗaya ne, hatta da yadin hijabinsu babu bambanci. Addu'ar buɗe taro aka yi, kafin nan aka kira shugaban makaranta domin yin bayanin tarbar baƙi, da kuma nuna farin cikinsa ga wannan rana. Bayan ya gama kuma ya ɗora da bada tarihin makarantar, kamar yadda kusan kowacce walimar sauka akan yi, shugaban makaranta yana bada tarihin makarantar. A sadda ya kai gaɓar aya a zancensa, ɗai-ɗaikun mutane ne ba su koka ba. Saboda da dama an san labarin Amrah, an kuma san sadda ta rasu. Sai ya zama kamar tsohon tabo ne aka fama musu. Maryama uwar kuka ma dasa nata ta yi, tunawa da labarin Amrah da ta yi, da kuma alƙawarin da ta kasa cikawa na ziyartar Umman Amrah da ta alƙawarta yi a kai a kai. Kamar an ce ta ɗaga kanta, ta hango iyayen Amrah tafe, fuskarsu ƙunshe da annuri. Hango shi da shugaban makarantar ya yi ya saka shi faɗin, "Ga mahaifinta nan ma ya iso, za mu so jin wani abu daga bakinsa." Da murmushi ya karɓi loud speaker ɗin, ya fara da sallama, sannan ya ce, "Duk da dai ban san me zan ce ba, kasantuwar mun zo a ƙurarren lokaci, duk da haka ba zai hana ni jawo hankulanmu ba, game da riƙo da Al'qur'ani, musamman ma ku ma su saukar nan..." Ya fuskanci masu saukar, yana jinjina kansa, sannan ya dora da faɗin, "Kar ku ga ai kun sauke, sai ku banzatar da karatunku, ku daina yinsa baki ɗaya. Al'qur'ani na da wani abu, da zarar ka bar shi da awa ɗaya, to zai bar ka da yini ɗaya. Idan ka bar shi da yini ɗaya, zai bar ka da sati ɗaya. Idan ka bar shi da sati ɗaya, zai bar ka da wata ɗaya. Idan kuwa ka bar shi da wata ɗaya, shi kuma sai ya bar ka da shekara. Idan ka bar shi da shekara, sai ya bar ka baki ɗaya. Shin za mu so littafi mai tsarki ya bar mu? Za mu so karatun da muka yi ya tashi a iska? Ba za mu so ba. To sai mu dage. Mu riƙe shi ƙyam, sannan kuma mu kiyaye sa. Kamar yadda manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce, mafi alkhairinku shi ne wanda ya san Al'qur'ani kuma ya kiyaye shi. Sai mu dage, mu jajirce, kamar yadda na tabbatar iyayenku sun ji daɗin wannan ranar, ina fatar su ci gaba da jin daɗi game da ku har ƙarshen rayuwarsu. Ku dage ku ma ku sanar da wasu, sai ku samu kwantankwacin ladar da za su samu yayin da suka aikata kyakkyawa. A daidai sadda muke isowa na ji bayanai daga bakin shugaban makaranta; silar buɗe ta, da kuma Amrah baiwar Allah, wacce har yanzu mutuwarta ta kasa kankaruwa daga zukatan dubban mutane. Rayuwarta ta zama abar da kowane uba zai yi burin ƴarsa ta zamto haka, kowacce uwa za ta so ƴarta ta kasance da wannan halayen. Ni ne mahaifin Amrah, kuma har yau har gobe na kasa daina shi mata albarka. Na kasa daina zubda ƙwalla da mutuwarta. Rayuwarta mai shiga zukata, haka kuma mutuwarta mai zama a zukata. A ƙarshe ina muku addua ya ku wannan ɗalibai, kuma ƴaƴaye a gare ni, da rayuwa mai albarka ta tabbata a gare ku. Allah ya albarkaci karatunku. Allah ya ba ku ikon amfani da shi har ƙarshen rayuwarku. Na gode." Ya ajje loud speaker ɗin haɗe da barin wurin, ya isa wurin zaman manyan baƙi, inda aka tanadar masa. Sosai bayanan Mallam Abdallah suka ƙara narkar da zukatan dubban al'umma. Kuka sosai ake yi a wurin. Daga nan aka ci gaba da gabatar da karatuttuka, yayin da ɗaliban ke fitowa ɗaya bayan ɗaya, suka karɓi kyaututtukansu. Ƙarfe ɗaya daidai aka kammala. Nan aka fara warwatsewa, yayin da ɗalibai masu sauka suka fara haramar yin tasu gagarumar walimar, ta yasu yasu kawai. Kafin nan sai da Maryama ta je wurin Umman Amrah, bayan sun gaisa ne Ummah ke mata murnan saukar tasu. Sosai Maryama ta ji kunya, ta ba Umma haƙuri a kan rashin komawarta, sannan ta mata alƙawari lallai za ta zo gobe, saboda akwai gagarumar maganar da take so su yi. Umma ta ce da ita babu komai ta kwantar da hankalinta, ai ta san yanayin hidimomin ne, bare kuma ita da take ɗaliba. Bankwana suka yi da Umma ta tafi, Maryama kuma ta nufi inda sauran ɗaliban suke. Amma fa rabi da rabin hankalinta na ga Modu da ta baro yau, tana jin kamar ba ta kyauta masa ba. *** 11th January 2010 Bama, Maiduguri. Zaune take tana ma wata budurwa wacce za ta kai kimanin shekaru ashirin susar kai. Suna yi suna ɗan taɓa hira, yarinyar na faɗin, "Aunty jiya Anas ya ce da ni wai ya kamata ya ga Abbu su yi magana. Wai gidansu ana ta masa maganar aure. To ni dai ban san me zan faɗa masa ba, ban kuma san ta hanyar da zan iya tunkarar Abbu da wannan maganar ba." Mahaifiyar tata ta ɗago yarinyar haɗe da komar da ita zaune. Ta ce, "Yamaira kenan. Wannan ai abun farin ciki ne, wanda ya kamata a ce kin faɗe shi ba tare da shakkun komai ba." Kunya ta ji wacce aka kira da Yamaira, ta rufe fuskarta ba tare da ta ce komai ba. "Yau zan faɗawa Abbunku, insha Allahu idan ya dawo. Duk yadda muka yi da shi zan sanar da ke, sai ki faɗawa Anas ɗin." Wani matashi ne ya shigo cikin falon, da faraa ƙunshe a saman kyakkyawar fuskarsa, ya ce, "Sannunku da hutawa Aunty." "Yauwa Sans. (Sunan da take kiransa da shi kenan, saboda tana kararsa sosai, kasantuwarsa ɗan fari ne. Sans kuma ya samo asali ne daga sunansa Salman Nasir Shuwa. Sai ya zamanto sunan ya bi shi, har ma an daina kiransa da Salman ɗin.)" "Yaya Sans wannan girl friend ɗin taka ta damen da kira fa. Kullum sai ta min kira aƙalla uku ko huɗu, kawai don a gaisa. Ni na gaji." Wani kallo Sans ya watsa mata, ya ce, "Ji min yarinya. Wato daga ma kin samu ana kiranki shi ne har da wani jan aji ko. Sannu kin ji." Murmushi ta yi haɗe da ɗaukar ribbom ɗinta ta fara faka yalwataccen gashinta. "Yamaira kamar wayata na ringing. Taimaka ɗauko min da sauri kar ta tsinke." Da saurin kuwa ta rashi ta ɗauko, sai dai bisa rashin sa'a har ta tsinke a lokacin. Kafin ta yi dialing mai kiran sai ga shi ya sake kiranta, da sauri ta gaggauta ɗauka da sallama a bakinta. Miƙewa tsaye ta yi bayan yin sallamar, cike da tsoro da firgici ta dafe gabanta. Zuciyarta na bugawa da sauri da sauri. Cikin muryar kuka ta ce, "Ina za mu tafi mu bar ka Abbu? Na kasa fahimtar komai da yake faruwa. Dan Allah ka sanar da ni." Su kansu yaran sun tsorata a wannan gaɓar. Gabansu sai tsananta duka yake, suna jin yadda duniyarsu ke juye musu. Sakin wayar ta yi tana kuka sosai, hakan ya sa Sans ya ɗauka haɗe da kara ta a kunnensa, sai dai ba ya jin komai sai wani sauti da yake ji, wanda ya kasa gasgata cewa sauti harsashin bindiga ne ke tashi. "Ku gaggauta guduwa Shereefa. Babu kwanciyar hankali a garin nan, ga su nan sun ƙariso inda nake. Idan sun kashe ni ki yafe min. Don Allah ku gudu kar ku zauna. Bomb suke tayarwa." Ƙit! Ya kashe wayar. Sans na ambatar sunan Abbunsu amma ina, shiru ya ji alamar ya kashe. Kuka suke sosai su duka ukun. Ita mamar tasu ma baje take a ƙasa tana kukan, ta kasa koda ƙwaƙƙwaran motsi. Cikin ƙarfin hali da muryar kuka Sans ya ce, "Aunty ku tashi mu san na yi. Abbu ya ce babu kwanciyar hankali a garin nan. Mu tafi tun abun bai iso nan ba." Da kanshi ya samu ya cicciɓi mahaifiyar tasu, sannan ya kama hannun ƙanwarsa Yamairah, ya ce lallai sai sun bar gidan yanzu. Hijabi ma shi ya saka ma Mamarsu, sannan ya kawo ma Yamaira tata ta saka, ko kuɗi ba su tsaya nema ba kawai suka bar gidan, hankulansu a tashe, tunanin Abbunsu kawai suke, da kuma makomarsu a wanann fitar da suka yi. *** To to to to! Yanzu dai na san na warware muku kawuna dangane da Salman da kuma Sans ba? Haha! Salman shi ne Sans, wato twin brother ɗin Annur kenan😀 An fara zuwa inda kuke so ko? Maryama ta fara koyawa Modu kalaman soyayya, wanda ba mu sani ba ko so take tsuntsun soyayyar Amrah ya dawo kanta?🤐 Yo anya ma dai Modu zai taɓa iya son wata bayan Amrah, da yake ganin kamar har yanzu tana nan da ranta? Ya maganar Sandra da ta ce za ta haɗa Maryama da likita? Shin wace magana ce Maryama za ta yi da Umman Amrah? Na san fa wasu sun manta da Ahmad Deedah, cousin ɗin Maryama ko?🤔 Ya kamata mu tuno shi haka nan. Wata ƙila akwai wata ƙarmaya ƙarmayar game da shi😷 Wayyo ni Fiddou ko a wanne hali take ciki yanzu?🤧 tana ba ni tausayi fa. Ga talauci, ga ƙiyayyar matar Yayanta, ga kuma uwa uba son maso wani da ta ɗorawa rayuwarta😰 ita ɗin ma fa ya kamata mu leƙo ta haka nan. Sannunku ghosts🤓 kawai sai a gama shan karatu amma a kasa kankaro mutunci ta hanyar dangwala alamar tauraron nan😎 kun kyauta ai. Na ga wasu na faɗin wai ba su ji daɗi ba ANS ya kusa ƙarewa, wa ya faɗa muku?🤔 anya ma dai ko rabi mun yi😅 kar dai kuma na shirgo ta fa😂 amma dai gaskiya akwai sauran labari. Kawai ku ci gaba da kasancewa tare da ni. Har da sugar zan daɗa ƙara ma labarin, yanda za ku ji shi da zaƙi zaƙwai kamar zuma😅. Thanks all. Pinky durling❤ RAZ 2 [8/30, 3:56 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 4⃣9⃣ Wattpad: PrincessAmrah Wannan shafin sadaukarwa ne a gare ki Faɗimatu Dawaki. Haƙiƙa ke masoyiya ce ta gaske, wacce nake alfahari da ita a kodayaushe. Ƙaunar da kike ma ANS har ta wuce gaban misali. Jinjina a gare ki, na gode ƙwarai da jajircewarki.😍😘 *** Sai daf da magrib sannan Maryama ta koma gida. A gajiye take lis, hakan ya sa kai tsaye ta nufi ɗakinta, a lokacin gidan nasu duk an watse, sai ɗai-ɗaikun mutanen da ba za a rasa ba. Tana fitowa daga wanka ta saka doguwar rigar barci, sannan ta ɗaura zani a kai, ta feshe jikinta da turare. Hijabinta ta saka har ƙasa sannan ta fito, ta tarar da Mama da ƙawayenta mutum biyu suna fira. Har ƙasa Maryama ta duƙa ta gaishe su, sannan ta nufi ɗakin da Modu yake. Zaune yake a ƙasa ya yi zaman dirshan, yana wasa da haruffan da Maryama ta ajje musamman tana koya masa karatu. Murmushi ya saki a sadda ya ganta, ya gaggauta miƙewa tsaye yana sake bin ta da kallo, ita ɗin ma kallonsa take. Jallabiya ce a jikinsa kalar coffee brown, sosai ta ma kyakkyawar ƙirarsa kyau, ya fito babban mutum mai tarin ƙwarjini, wanda idan har ba ka san shi ba, ko kuma an faɗa maka ba, ba za ka taɓa cewa mara hankali ba ne. "Ya Noor wannan irin shan kyau haka." Ta ƙarisa matsowa kusa da shi, tana masa fara'a. "Au shiru ma za ka min ba za ka min magana ba? Ko ka manta na faɗa maka yau an mana walima?" Sai a sannan cikin dariyarsa ta yaƙe ya ce, "Ban manta ba ai." Ya kama rawa da kansa, ya ɗan duƙar da kansa ƙasa. "To na ji, dawo nan ka zauna." Ta gwada masa bakin gadonsa da hannu. Babu musu ya zauna yana mata dariya, ya kai yatsunsa biyu a cikin baki yana tsotsa. Da sauri Maryama ta ce, "Amma Ya Noor don Allah ban hana ka cin hannun nan ba? Ba ka ga yadda kake komawa ba fa, kamar wani dolo." Ɗaure fuskarsa ya yi a wannan karon, tare da faɗin, "Ni ba dolo ba ne." Ya fiddo yatsun daga cikin bakinsa. "Yauwa ɗan albarka. Ko kai fa. Yanzu dai darasi za mu yi. Ka san wane iri?" Ya gyaɗa kansa da murmushi, yana matuƙar son darasin da suke yi ko ma wanne iri ne; na soyayya, ko kuma boko da arabi da take koya masa. "Yau wasu baituka ne na musamman na tsaro su domin masoyiyarka Amrah. Ina fatan za ka ajje hankalinka sosai ka saurara, kuma ka iya su don ba zan maka ƙari ba har sai ka maimaita su gobe na ji." Ɗaga mata kai ya yi yana dariya, ya ce, "Na yarda, zan iya sosai." "Yauwa fa, haka nake son ji. Ka shirya?" Kamar yadda ta saba ta masa wannan tambayar. "Ehh! Na shirya." Ya faɗa cikin waƙa, kamar yadda ta koya masa. "Ka tabbata ka shirya?" Ta sake tambayarsa. "Ehh, na shirya." Ya sake maimaitawa. Sai da ta faɗi haka har sau uku yana faɗin ya shirya, kafin ta yi gyaran murya tana faɗin, "Amrah nake so! Baiwarta nake so! Iliminta nake so! Halinta nake so! Fara'arta nake so! Kalamanta nake so!" Ya yi shiru ya miyar da kaf hankalinsa gare ta, bakinsa a buɗe yake har yanzu, fuskarsa ƙunshe take da fara'a. Sosai yake jin daɗin waƙar, yana jin wani irin yanayi a tattare da shi, wanda ba zai misaltu ba. Maryama ta ci gaba da, "Ni dai na ce sai Amra, Amrah kaɗai ce tai zarra, Kusancinmu ya wata da zara, Ita na bai wa dukka lamurra, Rayuwata tata ce ta ƙara, Ki dawo gare ni ya Amra, Kewarki nake ni Nura, Ke ɗai ce a gare ni Amra, A zuciya tawa nai shara, Na kakkaɓe ko'ina sai Amra!" A wannan lokacin kam sosai Modu ke lila ƙafafuwansa, yana lumshe idanuwansa cike da shauƙin ƙauna. Jinsa yake a wata sabuwar duniya, yana ƙara tuno wasu abubuwa da dama da suka shuɗe na rayuwarsa. Ita kanta Maryama jin ta yake sosai a zuciyarsa. Yana girmama darajarta, martabarta, da kuma ƙimarta. Saboda kyautata masan da take. Duk da ya kasance ba ya cikin hankalinsa, amma an halicci zuciya da son mai kyautata mata, da kuma ƙin mai munana mata. Kyautatawar da Maryama ke masa, take saka shi a nishaɗi dare da rana, ko Fiddou ba ta masa haka. Saboda ita ɗin ma tana neman mai saka ta farin ciki ne. A gida ma ba daɗi take ji ba, rayuwar tsanani take ciki sosai. To ta ya ta ga farin cikin da har za ta iya saka wani? A ɓangaren Maryama ma sosai ta ji daɗin ganin ta saka Modu farin ciki. Baki buɗe take kallonsa, tana sake maimaita baitukan tana tafawa, tana lila kanta ita ma alamar rawa. Da haka ta fara jiyo kiran sallar magrib, hakan ya sa ta masa bankwana haɗe da barin ɗakin, ta bar Modu cike da shauƙi da begen Amrarsa. *** Tunda suka samu nasarar fita daga gidan suke gudu gudu sauri sauri. Ko'ina suka gitta ya kaure da hayaniya. Mutane sai gudu ake domin neman tsira. Ƙarar tashin bomb kuwa ba a bakin komai yake ba. Haka ƙarar harbin bindiga ma, har sai su rasa ta inda yake tasowa. Sosai suka siƙe, hakan ya sa Yamairah ta duƙe dafe da ƙirjinta, sai famar shessheƙa take, tana hawaye. Kama hannunta ya yi Sans, cikin murya mai nunar da tsantsar tashin hankalin da yake ciki, ya ce, "Daure ki tashi mu tafi Yamaira, kin ga jama'a sai guduwa suke ana neman tsira. Kar mugayen nan su riske mu a nan." "Ba zan iya ta shi ba, zuciyata nake ji kamar za ta tsage, ku tafi kawai ku bar ni a nan, ko ku kawai ku tsira." Cikin tashin hankali mahaifiyarsu na kuka sosai ta ce, "Ki daina faɗar haka Yamaira, babu inda za mu tafi mu bar ki. Ki huta sosai sannan mu tafi." Ita ɗin ma ta duƙe a gajiye, tana mai bubbuga bayan Yamaira alamar rarrashi. Sosai ƙara ke sake kusantarsu, hankalinsu ya sake tashi. Sans da sauri ya ce, "Aunty ku daure mu tafi, ga hanyar da mutane ke bi can, wata ƙila mu samu wurin fakewa, tun ba su ƙariso inda muke ba." Da ƙyar ta miƙe mamar tasu, shi kuma Sans ya ƙoƙarta kama hannun Yamaira ta miƙe, sai dai kuma tana miƙewa ta sake komawa ƙasa ta duƙe. Hankalinsu in ya yi dubu ya tashi, musamman yadda abun ke ta sake kusantarsu. Ƙarar tashin bomb ke yawaita fiye da ɗazu. Duƙawa ya yi a daidai saitin Yamairah, cikin kuka ya ce, "Hawo bayana Yamairah, mu gaggauta barin wurin nan." Hawa bayan ma kasawa ta yi tsabar jigata da ta yi. Sai da Aunty ta taimaka mata sannan ta hau, cikin sauri suka ringa nufar inda suka ga al'umma na bi. Sun yi tafiya mai nisa kafin suka ci karo da wani kango, wanda da alama babu kowa a cikinsa, tsohon gini ne. Kallon wurin ya yi Sans, ya ce, "Aunty ko za mu je can, ga wasu a can ma da alama duk irinmu ne, sai kuka suke." Ba ta iya magana ba Aunty, sai dai kanta da ta ɗaga masa kawai, hakan ya sa suka ƙarisa shiga cikin kangon. Samu ya yi ya kwantar da Yamaira a ƙasa, yana mata sannu, sannan kuma yana ma Aunty ma sannu. Hankalinsu ya ɗan kwanta da zaman wurin, saboda ko hayaniyar ma ba a ji sosai, ƙarar tashin bomb ma sai dai su ɗan ji sautinsa kaɗan. Sun ɗauki kusan awanni biyar a wurin kuma sai tashin hankalin yunwa da ƙishirwa, ga shi kuma babu mai guzuri a cikinsu, ba su kaɗai ba, har sauran jama'ar da suke wurin ma. Yara ƙanana sai koke-koke suke, dattijawa kuma an haɗa kai da guiwa, ana ta ambaton sunan Allah. Dafe ƙirjinta ta yi Aunty, tana jin yadda yake mata ciwo sosai, yana barazanar tsagewa. Tun tana daurewa har abun ya ci tura, ta ringa ambaton inna lillahi a bayyane. Cike da damuwa Sans ya ce, "Aunty me ya faru da ke?" Ƙirƙiro murmushi ta yi da faɗin babu komai, don ta san ko ta faɗa masa bai da maganin matsalarta. "Aunty kina da damuwa tabbas. Don Allah ki sanar da ni." Cikin dauriya ta ce, "Ina jin alamun tashin ulcer'ta ne Sans. Yunwa nake ji, ga ƙishi." Ta dafe kanta tana zubda ruwan hawaye, duk iya ƙoƙarinta na ganin ta daure amma ta kasa. Kamar Yamairah na jira ita ma ta ce, "Aunty ni ma yunwa nake ji. Babu komai a cikina. Ga shi kuma a bakina ko yawu ba ni da shi, tsabar ƙishi da nake ji." Cikin dakiya Sans ya miƙe tsaye, ya zaro wayarsa da ya saka a aljihunsa tun kafin ya fita daga gida ɗazu, shi ya ma manta da ita kwata kwata. "Zan je in dawo Aunty." Takunsa ɗaya ya ji ta kamo ƙafarsa. da hannunta na dama. Cike da tsoro da firgici ta ce, "Ina za ka je Sans? Cikin wannan tashin hankalin za ka fita? Ka duba ka gani, kowa ya nutsu a nan, babu mai fita. Don Allah ka dawo." "Aunty ko na zauna dole zan fita. Rayuwa za ta ci gaba da tafiya a haka ne ba ci ba sha? Dole za a buƙaci wani abu. Don Allah ki bar ni na tafi " Gyaɗa masa kai ta yi cikin kuka sosai ta ce, "Idan ma ka tafi ɗin, da wanne kuɗi ne za ka samo mana abincin da za mu ci ɗin?" Aljihunsa ya gwada mata da faɗin, "Ga wayata nan a ciki, zan nemi mai saye Aunty, insha Alahu zan samo muku abinci da abin sha." "Hankalina ya kasa kwanciya da fitar nan taka Sans. Don Allah ba don ni ba, ka dawo ka zauna, wallahi na yafe." Durƙusawa ya yi har ƙasa, cikin kuka ya ce, "Aunty addu'a kawai za ki min, insha Allahu zan dawo lafiya. Zan kuma same ku lafiya." Gyaɗa kanta ta yi, ta ce, "Shi ke nan Sans, Allah ya bada sa'a ya dawo min da kai lafiya. Allah Ya maka albarka." Murmushi ya ƙirƙiro haɗe da barin wurin, yana yi yana waigen mahaifiyarsa da kuma ƙanwarsa. *** Hannunta ya kama na dama, yana jin yadda take shessheƙar kuka ƙasa-ƙasa, da takun da take yi a hankali. Cikin tausayi ya dube ta, ya ga yadda fuskarta ta kumbure tsabar kukan da ta sha, idanuwanta sun mata luhu luhu, sun kaɗa sun yi jajur. Cikin sassanyar muryarsa ya ce, "Halan sai yaushe ne za ki cire ma kanki wannan damuwa Fiddou? Modu dai ya tahi wurin danginsa, babu tabbacin zai dawo gare ki. A ganina sam, bai kamata ki kasa cire shi daga rayuwarki ba. Ki sani, ko warkewa Modu yai yi yanzu bai san ki ba, bai san da zaman ki ba. Cire shi daga ranki shi zai hiye miki zama alheri a kan wannan damuwa da kike ciki. Ki duba ki gani hwa Fiddou, yau kwananki shida a asibitin nan, kwance ba ki da lahiya. A kan mi Fiddou? Mi da ba za ki kai zuciyarki nesa ba?" Shiru ta masa kuma har a lokacin ba ta daina kuka ba. Ta sani sarai, gaskiya Mahmouda ya faɗa mata. Amma kuma ta yaya? Ta wacce hanya ce za ta bi don ganin ta cire Modu daga zuciyarta? Abu ne da ba ta da maganinsa, ya zauna a ranta matuƙa, wanda cire shi ba abu ne mai sauƙi ba. Da haka har suka ƙarisa gaban motar Mahmouda, ya buɗe mata gaban motar ta shiga, sanann ya zagaya shi ɗin ma ya shiga, ya tayarta. A gaban gidan su Fiddou ya faka motar, shi ya taimaka mata ta fito, sannan ya buɗe booth ya fiddo ƴan tarkacenta da ya saka a ciki. Tare suka shiga cikin gidan, tana gaba yana bin ta a baya, har suka ƙarisa daga ciki. Kasantuwar yammaci ne, a tsakar gida suka samu Yayanta da kuma Aunty Sahiya zaune, suna fira. A susuce take sosai, hakan ya tashi hankalin yayanta, cikin kiɗima ya miƙe tsaye, ya saki baki yana bin ta da kallo. Mahmouda ne ya gaishe shi, ya amsa ba yabo ba fallasa, sannan ya ba shi izinin zama. "Halan dai duk jikin Modu ɗin ne ya mai she ki hakan ga giɗe?" Ta ji muryar yayan nata ya faɗa, cike da mamaki. Ba ta iya furta masa komai ba, sai sake fashewa da ta yi da wani kukan mai ƙarfi, ta duƙe bisa guiwowinta. Cike da masifa Aunty Sahiya ta ce, "Ke do Allah de idan mutuwa yai yi ki hwaɗi ma mutane kuma ki muna shiru, ke tasa mu gaba sai wani kuka kike." Kamar zai ce wani abu yayan nata kuma dai ya kasa. Duƙawa ya yi a gabanta, cikin ƙanƙanuwar murya ya ce, "Ki shiru ke jiya, ki min bayanin abin da ya hwaru." Sai a sannan ta ɗago kanta da rinannun idanuwanta, ta ce, "Yaya ko kaɗan ba ka damu da ni ba. Ka kasa cika alƙawarin da iyayenmu suka bar ma kahin su rasu. Yanzu yaya ashe kana cikin garin nan, na yi kwana da kwanaki ban dawo gida ba, amma ka kasa neman inda nake, kuma kana nan hankalinka kwance?" Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke, ya ce, "Ba haka ne ba Fiddou. Ai na san kina lahiya, tunda jinyar Modu ce kike yi." Gyaɗa kanta ta yi Fiddou, ba tare da ta furta komai ba ta ci gaba da kukanta. Mahmouda ne ya ce, "Yau kwananta shida ba ta da lahiya. Modu ma dangi nai sun taho gobe sati guda kenan sun tahi da shi. Tun bayan nan kuma ita ma babu lahiya, aka ba ta gado." Sosai ya ruɗe Yayanta, ya ma rasa me zai faɗa. Sai ya kalli Fiddou kuma ya juya ya kalli Sahiya. Jin sa yake kamar zai yi kuka, da gaske Fiddou take, tun bayan aurensa da Sahiya ko kaɗan bai taɓa kyautata ma Fiddou a matsayinta na amanarsa ba. Kullum cikin wahala take; gare shi da kuma matarshi. Dafe kansa ya yi, ya rasa uwar ubansa, can ya jiyo muryar Mahmouda ya ce, "Idan babu damuwa Yaya akwai maganar da nake so mu yi da kai." Ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi, yana jin yadda zuciyarsa ke masa zafi. Baƙin ciki ya taru ya ƙunshe a cikin ransa. "Ina sauraren ka." Yayan ya faɗa tare da ƙura masa idanuwa. Yana mai jin duniyarsa ta masa tsanani, tsanani mai wuyar a fasalta shi. Readers, sannunmu sannunmu da jimurin karatu😀. Wannan shafin bai yi tsawo sosai ba, na sani. Sai ana haƙuri da ni, kun san jiki da jini, ba kullum mutum ke da cikakkiyar lafiya ba. Idan ma akwai ta cikakkiya, to akan samun canjin mood, yau rubutun da daɗi, gobe kuma babu. Me kuke tsammanin zai faru? Menene Mahmouda zai faɗa ma Yayan Fiddou? Alheri ne ko sharri😱? Allah sa dai abun kirki ne. Da gaske fa ina tausayin Fiddou har cikin zuciyata. Har ma na rasa gane shin ita da Annur waye soyayya ta fi zautarwa? Annur ne, na sani. Amma fa ita ɗin ma ta zauce, mahaukaci take ma wannan muguwar soyayyar da har ta kwanta kwanaki shida a asibiti kawai saboda tafiyarsa. Soyayya is real, I know. Wadda duk da faɗa tarkonta sai dai addu'a kawai, don kuwa ba wuya ta zautu, barinma dai ta tsakani da Allah, wacce babu surki ko kaɗan a cikinta.🤧 Where are the lover birds? Kun ji waƙar soyayya wadda Maryama ta koyawa Modu ba? Haha! Ƙirƙirarra ce daga bakin Amrah marubuciyar, ta ƙirƙira ta musamman don takwararta Amrah.🤣 Thanks all my fans. Ina ƙaunarku all fisabilillah😘😍 Comment, vote and share with your family and friends. Pinky durling RAZ 2 [8/30, 3:57 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 5⃣0⃣ Wattpad: PrincessAmrah Wannan shafin naku ne baki ɗaya ƴan NAGARTA WRITER'S FANS GROUP. Musamman Meinerh, Ummu Ikhram, Ummu Aysher and Janaaht. Sannunku da rero baitocin Amrah😂 kun ƙoƙarta fa irin sosai da sosai ɗin nan😍😘. Ina yin ku sosai, ina ƙaunarku all fisabilillah. *** Tunda ya bar wurin gabansa ke dukan uku-uku. Sosai yake ji kamar wani abu zai faru, sai dai kuma ya kasa tantance menene zai faru ɗin. Tausayin mahaifiyarsa da ƙanwarsa tilo yake. A wani sashen na zuciyarsa kuma tunanin halin da mahaifinsu yake ciki yake. Tunawa ya yi da kalaman Abbun nasa na ƙarshe, da kuma sautin harbin bindiga da ya ji, wanda ya kasa fita daga cikin kunnuwansa. Ko dai an kashe Abbu ne? Ya tambayi zuciyarsa. Rashin samun amsa daga gare ta ya sa ya gaggauta kawar da tunanin daga zuciyarsa, gudun kar ya kai wa bango karo ba tare da ya sani ba. Tashin hankalin da ke akwai yanzu kamar ma ya fi na ɗazu. Guje gujen da al'umma ke yi domin su tsira da rayukansu har ya fi na ɗazu. To a hakan zai samu mai siyan wayarsa? Ƙara sauri ya yi da haka har ya isa titi. Abun hawa ma babu, kowa neman ceto yake. Tafiya ya ci gaba da yi a hankali saboda gajiyar da ya yi. Sai kuma ya tuno da halin da ya baro mamansa da ƙanwarsa a ciki; yunwa da kishirwa. Cikin sauri ya ci gaba da takun nasa, har Allah ya haɗa shi da wani mai taxi ya zo wucewa. Saurin dakatar da shi ya yi, amma ina, cike take da al'umma, wasu kan wasu. Har sun yi nisa kuma sai ga su sun dawo, cikin tausayi dreban ya kalle shi haɗe da furta, "Idan za ka iya daurewa da zaman matsatsi mutum ukun nan da ke gaba su gyara maka ka zauna, ko a kan ɗaya ne. Ya fi tsayuwa a nan ɗin, cikin tsananin tashin hankalin nan" Bai ko ba shi amsa ba ya buɗe motar, suka gyara masa ya zauna a kan wani. Ta titin suka bi kai tsaye, saboda sojoji ne rinkis a bakin hanyar, masu tsaron mutane. Duk inda suka gitta sojoji sai sun musu bincike kafin su bar su su tafi. Sun yi tafiya mai nisa kafin motar ta tsaya musu. Dreban ya yi ya yi ta tashi amma ta ƙi tashi, hakan ya tabbatar masa da cewa mai ne ya ƙare. Kansa ya dafe cike da takaici da faɗuwar gaba. Hawaye ke neman fitowa daga idonsa, saboda a tsakiyar daji suke, suna daf da shiga cikin Maiduguri. Dama kuma plan ɗin Sans kenan, su ƙarisa cikin gari ya samu mai siyan wayarsa, saboda babba ce sosai, mai tsada. Cikin wata irin murya dreba ya labarta musu abin da yake faruwa. Salati aka ɗauka duka motar, barinma matan da ke ciki, kuka suka fasa mai nuna tsantsar tashin hankalin da suke ciki. Babban abun takaicin kuma babu soja ko ɗaya a kusa kusa, wata ƙila sai gaba ko suna cin karo da soja. A tsorace suke su duka, tsoronsu ma kar kar ƴan ta'addan su ɓullo musu ta tsakiyar daji, sun tabbata sun tashi aiki daga nan. Mazan da ke cikin motar ne suka firfito, a tunaninsu wai ko za su samu wata mota ta zo wucewa a taimaka musu a samo mai ko za su samu barin dajin. Matan kuma cikin motar suke zaune. Zuciyoyinsu a dagule, sun ga samu sun ga rashi. A ɓangaren su Yamaira kuwa, tun bayan tafiyar Sans jikin Aunty ya ƙara tsananta. Dafe take da ƙirjinta, tana jin tsananin ciwo a cikinsa. Dama haka ulcer take mata, matuƙar ta ji yunwa mai tsanani to akwai matsala. Ta ringa shan wahala kenan tana aman jini, har sai ta samu ta ci abinci, ta ɗora da maganin da take sha; ulcer kit. To yanzu babu ma abincin bare maganin. Ga ƙishi ko yawu babu a bakunansu. Ba Yamairah kaɗai ba, hatta sauran mutanen da ke wurin hankulansu sun tashi da ciwon Aunty. Sun dawo kanta baki ɗaya, suna tausaya mata. Ga shi duhu har ya fara, an rasa samun mai fita daga wurin don ganin halin da ake ciki. Suna cikin haka suka fara jin ƙarar motoci, hakan ya sa suka ƙara firgita, suka dabaibaye juna, banda sautin ajiyar zuciya babu abin da ke fita a tsakaninsu. Kamar a mafarki suna fara jin sautin bindiga, ga ƙarar taku ana kusanto cikin kangon. "Ga wasu nan." Suka jiyo muryar wani matashi ya faɗa, hannunsa riƙe da bindiga. Nan fa ake yin ta. Daga masu sakin fitsari sai masu sakin zawayi. Abin da suka jiyo labarinsa ne daf da su yanzu. Nan fa suka sadaƙas, dukkansu suka kwakkwanta a ƙasa. Bataliyar mutanen ce ta shigo, su kusan talatin ko ma fin haka, kowanne riƙe da bindiga, fuskokinsu a doɗe, ƙwayar idonsu kawai ake gani. Wani babba daga cikinsu ya sa duk suka tashi zaune, kusan al'umma arba'in ne, duk suka ɗaɗɗago suna kuka. Ƴan matan da ke ciki suka fitar, su shida, ciki har da Yamaira. Mutum biyu suka tisa ƴan matan gaba suka wuce da su, sauran kuma aka saita bomb kusa da wani dutse, ba tare da kowa ya sani ba, sannan suka bar wurin. Kuka sosai iyayen yaran ke yi, a ganinsu su sun tsira, yaran ne kawai aka tafi da su. Baki ɗaya Aunty ji tai gwara ma mutuwa ta zo ta ɗauke ta, zai fi mata sauƙi fiye da wannan halin da take ciki. Ga ciwo ya addabe ta, ga kuma uwa uba ƴarta da aka tafi mata da ita, ba ta san halin da take ciki ba. Sans ma ya tafi fin awa biyu, babu shi babu alamunshi. Mijinta ma babu labarinshi. Wannan fa shi ake kira da shiga uku! Sunan Allah suke ta ambata kawai, shi kaɗai ne Zai iya fitar da su daga halin da suke ciki. Wata irin ƙara suka ji a kunnuwansu, kafin wurin ya kama da wuta, ta mamaye kaf ilahirin wurin, har ma ta kai nesa da kangon. A take duk suka mace, ko gawarsu babu alamarta, saboda wuta ta gama soye su. *** Washe gari da misalin ƙarfe goma na safe ya ɗauki wayarsa, safe da ƙirjinsa, ya latso kiran Maryama. Sau kusan biyar yana kiranta amma ba ta ɗauka ba. Haka ya sa ya ajje wayar, a fili ya furta, "Please help and pick my call Maryam. I seriously neet to hear your voice. Am missing you so badly." Ya dafe kansa, hawaye na zirara daga idanuwansa. Annur da ke gefensa ya ce, "Na rasa gane kanka Guy. A maimakon ka ji da ciwon da yake damunka, ka tsaya ta wata mace, macen ma wacce sam ba ta damu da kai ba. Me zai hana ka fita a harkarta?" Gyaɗa kansa ya yi Bobby, ya ce, "Ba za ka gane ba ne guy. I love Maryama har ma ban san ta hanyar da zan misalta maka ba. Maryam is my choice, ina ƙaunarta, kamar idan na ji muryarta zan samu sassaucin ciwon nan da nake ji tun daga zuciyata. And...I want to tell her something before..." Ajiyar zuciya ya sauke Annur, haɗe da dakatar da shi ya ce, "To Allah kyauta maka. Ni bara na tashi, wurin aiki zan je." "Ok guy, please pray for me, Allah sa Maryama tai picking call ɗina." "Ameen." Annur ya faɗa cike da tausayin abokinsa, wanda ya gama ramewa a ƴan kwanaki ƙalilan, kamar ba shi ba. Ci gaba ya yi da kiran Maryama amma shiru ba ta ɗauka ba, shi kuma ya kasa haƙuri. * A gefensa take zaune, tana jera alphabets a gabanshi, fuskarta ƙunshe da murmushi. A-M-R-A-H ta jera, ta ɗago tana kallonsa, shi ɗin ma fuskarsa ƙayace da murmushi, wanda ke ƙara bayyana kyawunsa. Muryar Mama ta ji tun daga nesa tana faɗin, "Maryama wayarki na ta ringing fa tun ɗazu. Zo karɓi ga ta." Miƙewa ta yi Maryama, a daidai bakin ƙofar ɗakin ta karɓi wayar da fara'a, a lokacin ma har ta tsinke. Koda ta duba 12 missed calls ta gani, baki a sake take dudduba mai kiran, duka mutum ɗaya ne. A bayyane ta furta, "Bobby!" Kafin ta fara tunanin ajje wayar sai ga wani kiran nasa ya sake shigowa. Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta ɗauka, da sallama ƙunshe a bakinta. "Maryama mutuwa zan yi, ki taimaka ki saurare ni, wata ƙila maganar ƙarshe ce za mu yi da ke." Wannan maganar tasa ba kaɗan ɗin karyar da zuciyar Maryama ta yi ba. Take ta ji hankalinta ya tashi, duk da ba sonsa take ba. Muryarsa kawai idan ka ji ta isa ta tabbatar da ingancin maganarsa, lallai bai da lafiya, akwai abin da yake damunsa. "Lafiya Bobby, me ya same ka?" Ta faɗa cikin rawar murya. Runtse idanuwansa ya yi duka biyun, ya ji daɗin saurarensa da za ta yi, ko ba komai jin muryar Maryama kaɗai kan saka shi cikin shauƙi, shauƙin ƙauna. "Ɗaya daga cikin manya manyan munanan halayena ne Maryama, smoking ne ya ja min, shi ya kai ni a wannan mugun ciwon da nake, wanda ba lallai na ci gaba da rayuwa ba." Canza wayar ta yi daga kunnen dama zuwa na hagu, idanuwa a buɗe tamkar yana a gabanta, ta ci gaba da saurararsa, "Maryam ina ƙaunarki, ke ce mace ta farko a rayuwata wacce na fara so tsakani da Allah, haka kuma ba na ji akwai wacce zan so bayanki. In short, na tabbata ina daf da mutuwa, ba zan samu kamarki ba har na koma ga Allah maɗaukakin sarki. Alfarma ɗaya nake nema a wajenki, wacce ita ce silar kiranki ma baki ɗaya." Sosai take tausaya masa. Ita ɗin dama uwar hawaye, babu wuya kuwa ruwan hawaye ya fara sintiri daga idanuwanta zuwa kumcinta. "Akwai wani abokina, sunansa Annur, ina so na sadaukar masa da soyayyarki, saboda ba ni da tamkarshi a duk cikin abokaina. Ƙaunar da nake masa ta sa nake son sadaukar da abin da na fi matuƙar so a rayuwata, ke kenan. Don Allah ba don ni ba Maryam, ba don halayena na banza ba. Ki taimaka ki amince da wannan buƙatar tawa, ki auri Annur, dama gidansu an daɗe ana so ya fitar da matar aure ya yi aure. Kar ki watsa min ƙasa a ido Maryama, zan baki lokaci ki yi tunani, idan har ina da sauran numfashi zuwa gobe zan kira ki. Na bar ki lafiya." ya tsinke kiran, ba tare da ya jira me za ta kuma faɗi ba. Sandarewa ta yi a zaune tun sadda ta ji buƙatarsa. Har cikin zuciyarta tana tsananin jin tausayin Bobby, tana jinsa har cikin zuciyarta. Sai dai kuma ta rasa dalili, ta rasa a wane babi yake a zuciyarta. Duk da hakan, ba ta jin za ta iya amincewa da wannan buƙatar tasa. Ba za ta taɓa iya auren fake Annur ba. Mutumin banza, wanda ya zauna a wani gida don yaudara, a matsayin asalin yaron gidan. Modu da ke zaune gefenta duk sai ya sha jinin jikinsa. Ya kasa yi mata magana, saboda halin da ya ganta a ciki. Haka kawai yanayin nata sai ya tuno masa wani sashe na rayuwarsa. Sosai ta tuno masa wani lokaci da ya shuɗe, a tsakaninsa da Amrah. Lokacin da yana Cyprus suna waya, ciwonta ya tashi, bayan sun yi waya take shaida masa halin da take ciki, har ma an kwantarta asibiti. Ya shiga damuwa sosai, kuma yanayinsa ya sauya. Shi ya sa yake kallon Maryama a matsayin wacce masoyinta yake cikin damuwa, damuwa mai tsananin gaske. Sosai yake jin kansa na sara masa. A duk lokacin da zai tuno da wani abu na rayuwarsa, take zai ji kansa na masa ciwo, komai yana juya masa, zuciyarsa na masa tuƙuƙi, abun ba ya misaltuwa. Ganin halin da yake ciki ya sa Maryama ƙarfin halin wartsakewa, cikin dakiya ta ce, "Ya Noor miye ne kuma? Ko ba ka da lafiya ne?" Idanuwansa a runtse ya ce, "Ba ke ce ba..." Ya yi shiru ba tare da ya ƙarisa zancen ba. "Ni ce me? Faɗa min ko kuma mu ɓata." "Ke ce kike kuka. Kuma kin ƙi ki faɗa min ko me aka miki." Murmushi ta ƙirƙiro na dole, ta ɗora fararen idanuwanta da suka rine zuwa launin ja a cikin nasa. Wani irin kallo take masa mai kashe jiki. Ta ɗan tauni leɓonta, sannan ta ce, "Ba wani abu ba ne ba fa. Tsakuwa ce ta faɗa min a ido." Gyaɗa kansa ya yi alamar a'a, bai yarda ba. Bai kuma faɗin komai ba, sai dai har yanzu bai daina jin wani iri a zuciyarsa ba. * Cikin murya ƙasa ƙasa ya ce, "Yaya idan babu damuwa, so nake ka ba ni auren Fiddousi." Ba yayan kaɗai ba, ita kanta Fiddou tsayar da kukan nata ta yi ta ɗora idanuwanta a kansa. Ta gagara furta komai, sai dai bakinta na motsi, alamar tana son yin magana. "Tun daga ranar da na kaɗe Modu da mota, na hwara ɗora idanuwana a kan Fiddou, na kamu da ƴaunarta, ƙauna mai tsanani. Tun ranar na saka ta a zuciyata. Sai dai kuma na bar abun zaune a raina, ba don komai ba sai don soyayyar da na ga tana yi wa Modu. Ta sadaukar da komai nata saboda samun lahiyar Modu. Ta shiga tsananin damuwa a lokacin da aka hwaɗi matsalar Modu. Wanann dalilin ne ya sa na yi shiru, na ci gaba da dakon sonta. Soyayyar maso wani na ɗawainiya da duk wani saƙo na zuciya da gangar jikina. Abin da ke ƙara ingiza soyayyar Fiddou a cikin zuciyata shi ne, tausayinta da nake. Ina matuƙar tausayawa rayuwarta. Sosai farin ciki ya yi ƙaranci a rayuwar Fiddou. Baƙin cikin da take ƙunsawa zuciyarta ya fi farin cikin yawa. Wannan tausayin nata da nake shi yake ƙara rura wutar ƙaunarta a cikin zuciyata. Dalilin da ya sa na daure na hidda zancen daga zuciyata ganin Modu ɗin ya tahi, dangi nai sun tahi da shi, na tabbata ba zai taɓa dawowa inda Fiddou ba. Soyayyar da Modu ke ma Amrah ba za ta taɓa bari ya so wata ɗiya mace ba, koda kuwa a ce bayan ya dawo hayyacinsa ya tabbatar da bata raye ne. Idan ma ya yarda ya auri Fiddou, rayuwa da shi za ta mata wahala. Ga uwa uba al'adunmu da nasu ba ɗaya ba. Akwai abin da za ta yi mai a ganinta ba komai ba, shi kuma a gare shi komai ɗin ne. Ina so na shiga rayuwar Fiddou. Ina so na hwaranta mata. Ina son bata hwarin cikin da duk ta rasa a rayuwarta. Ina son gusar da damuwa da baƙin cikin da ta cusawa rayuwarta. Don Allah yaya kar ka ce mini a'a. Kar ka butulce wa buƙatata." Yana direwa nan ya miyar da kallonsa ga Fiddou. Cikin marairaice murya ya ce, "Fiddou...!" Ta dakatar da shi da hannu. Hakan ya sa ya yi shiru, ya ci gaba da bin ta da kallo. "Ashe ba don Allah ne kake taimakona ba? Ashe don da wata manuhwa ce a ranka yas sa kake kula da ni? To na ji, ya ishe ka haka nan. Don Allah ka tashi ka tahi, ni ba ta kai nake ba..." Kuka ya ci ƙarfinta, da ƙyar ta iya dakatar da shi, ta ce, "Annur nake so! Annur zan aura! Babu wani a zuciyata bayan Annur." Ta shanye ruwan hawayenta, ta ci gaba, "Idan ma ka zo da wasu kalamanka na yaudara ne don in cire Modu daga zuciyata to ka lallaɓa ka tallabe su ku tahi tare. Ko Modu ya so ni ko ya ƙi ni, in dai zai aure ni bani da damuwa. Rayuwa da wani bayan Modu dai ce ba zan iya ba. Matuƴar na auri wanda ba shi ba, lallai za a neme ni a rasa, don kuwa zan tafi inda ba zan sake ganin wani ba, har rayuwata ta idasa a can." "Ba ma za a yi haka ba." Mahmouda ya faɗa haɗe da miƙewa, "Bari in tahi Yaya. Babu komai, Allah ya haɗa kowa da rabo nai." Kama hannunshi ya yi yayanta ya zauna, ya ce da matarsa ta kawo ma Mahmouda ruwa, ya sha su yi magana. *** Washhh Allah na! Na gaji. Ba laifi na sha typing fa. Ma haɗe wani lokacin, for now dai kam, na gama.😀 Thanks masoyana.😘 Kar ku manta fa a ringa yi ana kankaro mutunci ta hanyar dangwala tauraruwar nan ta hannun hagu.😀 Pinky durling RAZ 2 [8/30, 7:35 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 5⃣1⃣ Wattpad: PrincessAmrah *** A nan inda suke har duhu ya fara, rana ta fara ƙoƙarin faɗuwa. A wannan lokacin kam matan da suke cikin motar ma kuka suke. Su kansu mazan ba ƙaramin jarumta suka yi ba. Kowannensu ya buga uban tagumi, ana zancen zuci. Tagumin ya rafka shi ma Sans. Ya fara tunanin halin da ya baro mahaifiyarsa a ciki, da kuma yadda take shiga tsananin ciwo idan ulcer'rta ta tashi. Da kuma ƙanwarsa Yamaira, ta daɗe da jigatuwa ita ma. Bai san sadda ya fashe da kuka ba. Kuka mai ƙarfi, mai cike da zafafan ruwan hawaye. "Yaro ka yi haƙuri ka ji? Be strong. You're a man, don't act like a woman. Just look at how the women are crying, and you, kai ma kukan kake. What's the different between you and them? There's no! Don Allah ka yi haƙuri, mu taru mu dage da ambaton sunan Allah, muna sanar da shi halin da muke ciki. Mu haɗu mu ma matan can nasiha, tare da nusar da su cewa kuka babu maganin da zai mana baki ɗaya." Wani dattijo da suka zauna a gaban mota tare ne ya ma Sans wannan maganar, cike da ƙarfafa masa guiwa. Rage ƙarfin kukan nasa ya yi Sans. Ya dubi mutumin da idanunsa da suka kaɗa suka yi jajur. Cikin wata disasshiyar murya ya ce, "Baba ya zan yi? Mahaifiyata na can cikin wani hali, yunwa da ƙishi har suna neman galabaitar da ita, ga shi kuma dama tana da matsananciyar ulcer. Ƙanwata ta jigatu, har tafiya ma ba ta iyawa da kanta. A cikin kunnuwana na ji harbin bindiga, wanda ya kawo ƙarshen wayar da nake yi da Abbuna. Na baro su ne cikin wani tsohon gini, da nufin in samu masu siyan wayata, ko zan sama musu wani abu su saka ma cikkunansu. Baba ga ni a nan, mota ta tsaya mana, mun rasa mafita. Ba dole na yi kuka ba?" Kansa ya gyaɗa dattijon, sosai ya tausayawa yaron, musamman ma jin har da yarinya budurwa, yadda ƴan ta'addan suka dage tafiya da ƴan mata, abun ba a magana. Cikin sanyin murya, mai nuna kwantar da hankali, dattijon ya ce, "To ai ba kuka za ka yi ba, haƙuri za ka yi ka bar wa Allah lamurranSa. Ya san halin da muke ciki, kuma Shi zai fitar da mu. Idan Allah Ya sa mun samu taimako, mun samu man da zai fidda mu, na maka alƙawarin ni zan ba ka kuɗi daga aljihuna ka nemi wani abu ka siya musu, ba ma sai ka siyar da wayarka ba. Akwai kuɗi a hannuna, ni ma motar tawa lalacewa ta yi, wani aiki ya shigo da ni garin, ashe tsautsayin wahala ne ya shigo da ni." Godiya sosai ya masa Sans. Daga nan suka ci gaba da ambaton sunan Allah, suna masu ƙanƙan da kawunansu. Kamar an ce Dreba ya ɗaga kanshi zuwa titi, tun daga nesa ya hango wata hilux na dosowa daga cikin garin Bama. Kuma dukkan alamu sun nuna cewa ta sojoji ce. Hakan ya sa ya gaggauta sanar da sauran, suka tashi a tare suka nufi bakin titin. Hannuwa suke ɗagawa su duka, cikin sa'a kuma hilux ɗin ta tsaya, wacce sojoji ne maƙil a cikinta, har a bodinta. Tambayarsu suka yi abin da ke faruwa, take suka zayyane musu komai, da kuma tsawon awannin da suka ɗauka a wurin. Babu wani tiyo wanda za su sa a zuqo mai, hakan ya sa Ogan nasu ya umurci sojojin da ke cikin motar, da su koma cikin bodi, wancan matan su shigo ciki, mazan kuma su yi skwatin a bodin. Da babu gwara ba daɗi. Abin da ya faru ɗin kenan kuma. A haka suka ƙarisa cikin garin Maiduguri. Suna shiga garin suka sassauka, a take dattijon nan ya ciri kuɗi masu yawa ya miƙawa Sans, ya masa fatar alkhairi sosai, tare da jaddada masa cewa sai ya bi a hankali wurin shiga garin Bama, musamman ma yanzu da dare ya yi. Godiya ya masa Sans, sannan ya tari mai mashin, ya kai shi wata restaurant mai kyau. Abinci mai rai da lafiya ya sa aka masa take away, kusan wanda mutum goma za su ci, shi bai ma da nutsuwar cin abincin, ruwa kawai ya sha, sannan ya sai musu lemuka da yawa, ya kama hanyar tafiya. Kai tsaye tashar mota ya dosa, inda zai samu motar Bama. Sai dai kuma a rashin sa'a, bai samu motar ba. Ga su nan jere birjik, amma duk sun ce ba za su shiga Bama a wanann lokacin ba, saboda abubuwan da suke wakana a can ɗin, duk suna da labarinsu. Kuka yake sosai Sans ya marairaice fuska, ya zaro duka sauran kuɗin da mutumin ya ba shi, wanda za su kai darajar naira dubu ashirin da biyar. Dubu ashirin ya fitar daga ciki, sannan ya miƙa su ga wani dreba, ya ce ya taimaka masa ga kuɗin duka, ya taimaka ya kai shi. Firfir mutumin nan ya ce ba zai je ba. Wayarsa ya zaro daga aljihu, ya haɗa da kuɗin yana kuka, ya ce ya taimaka ya kai shi. Baki ya washe mutumin, ya ƙare ma wayar kallo. Babba ce ba ƙarama ba, sosai za ta yi kuɗi idan zai siyar. Cikin murya ƙasa ƙasa ya ce, "Na amince zan kai ka, amma bisa ga sharaɗin a bakin gari zan ajje ka idan mun isa, ba zan shiga ciki ba." Saurin ɗaga kansa ya yi Sans, ya ce, "Na amince wallahi." Haɗe da hanzarin ɗaukar ledojin abincin, ya bi bayan mutumin suka isa wurin motarsa. Yana jin yadda abokan aikinsa ke masa magana kan cewa kar ya je, amma ina, bai ko saurare su ba ya ƙeƙashe, suka kama hanyar Bama. *** Ruwa mai sanyi ya kora Mahmouda, yana mai tsananin jin ɗaci da raɗaɗi a cikin zuciyarsa. Me ya sa Fiddou za ta masa haka? Dama abin da ya jima yana ji ma tsoro kenan. Shi ya sa tun asali shi bai yarda da soyayya ba. Bai kuma taɓa shiga ƙanginta ba sai a yanzu. "Mahmouda ka yi haƙuri da duk kalaman da ka ji sun fito daga bakin Fiddou ka ji? Yarinya ce. Ita har yanzu gani take kamar soyayya da mahaukaci zai yi riba a gare ta, wanda kuma sam, hakan ba mai yiuwa ba ne a gare ta. Ina so ka ci gaba daga inda ka tsaya, tunda dai duk tsiyarta ai ba za ta taɓa ci gaba da rayuwa a haka babu aure ba. Na tabbata Modu ya tahi kenan, ba zai dawo gare ta ba. Ka ba ni daga nan zuwa mako guda, zan tari kawunmu da maganar, na tabbata zai tsawatar mata, zai kuma aura maka ita, saboda ni kam har ga Allah na yarda da nutsuwarka." Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke Mahmouda. Ya kalli ƙofar da ya ga Fiddou ta shiga, bai ko hange ta ba. Murmushin ƙarfin hali ya yi, haɗe da furta, "Amma Yaya ba ka tunanin wani abu zai iya hwaruwa idan aka mata dole? Yanzu hwa lokaci ne da aka daina yayin auren dole, gwamma dai a bar ta ta zaɓa da kanta, gudun samun matsala." "Kar ka damu kanka Mahmouda. Fiddou ba ita tai yi kanta ba, muna da magabata, wanda dole ne ta ji maganarsu. Don haka ka ƙyale duk wannan tunanin, tana da sauƙin kai sosai, kawai dai damuwa ce da tai yi mata yawa. Kawai dai ka ci gaba da lallaɓarta, namiji kake, ka san hanyoyi da yawa da za ka iya shawo kan mace." "Haka ne Yaya. Allah ya taimaka mana." "Ameen ameen Mahmouda. Ka tafi kawai, bayan sati guda ɗin sai ka dawo." Miƙewa ya yi Mahmouda. Fuskarsa a sake ya ma Yaya da Aunty Sahiya bankwana, ya kama hanyar fita. * Miƙewa ta yi a bisa ƙafafuwanta, fuskarta ɗauke da murmushi, ta kalli Modu da faɗin, "Zan je in dawo Ya Noor. Ka min addua." Murmushi kawai ya yi ba tare da ya ce komai ba, ya bi ta da kallo har ta fice daga ɗakin. A falo ta tarar da Mama tana kallo. Ta ce, "Mama shiryawa zan yi yanzu, gidan su Amrah da na faɗa miki zan je nake son zuwa." Mama ta ce, "To madalla. Kar ki manta fa, ki sanar mata duk halin da ake ciki, wata ƙila akwai wata gudummuwa da za ta iya bayarwa wurin samun warakar Annur." "Insha Allahu zan faɗa mata Mama." Ta tashi ta shige ɗakinta. Green ɗin atamfa ce ta saka mai zanen ganye pink. Ɗinkin riga da skirt ne da ya karɓi jikinta. Ɗaura ɗankwalinta ta yi sannan ta zira pink hijab iya guiwarta, ta shafa turaren humra, ta fito daga ɗakin hannunta riƙe da wayarta. Ɗari biyar Mama ta bata, sannan ta mata fatar alkhairi ta fita. A bakin ƙofa ta ci karo da Mahaifinta da kuma Yayansa, suna ƙoƙarin shigowa. Da faraa a fuskarta ta duƙa har ƙasa ta gaishe su. "Kawu Imrana an dawo lafiya?" Ta furta kanta sunkuye ƙasa. "Lafiya ƙalau Maryama. Sannu kin ji. Ina ta ganin saƙunanki ta inbox duk Friday na happy Friday ai. Allah ya miki albarka." "Ameen Kawu." "Sai ina?" Abba ya tambaye ta. "Zan je gidan su Amrah ne Abba. Jiya da muka haɗu wurin sauka duk sai na ji kunya. Ban koma ba fa tun ranar farko." Abba ya ce, "Lallai fa ya kamata ki je kam. Ba jimawa zan yi a gidan ba Office zan koma ai da kin tafi da motar, Mallam Ya'u kuma a can Office na baro shi." "Babu komai ai Abba. Zan hau napep." "To Allah ya tsare. Ki gaishe su." Miƙewa ta yi tsaye haɗe da ambatar to, sannan ta tafi. Isar ta gidan su Amrah ta samu Umma zaune da baƙuwa a tsakar gida. Jin sallamar Maryama ya sa Umma sakin murmushi haɗe da amsa sallamar, tana mata sannu da zuwa. "Iso daga ciki ƴata. Ga tabarma ki zauna." Da faraa Maryama ta zauna bisa tabarmar, sannan ta gaishe su. Amsawa suka yi su duka biyun, baƙuwar ta miƙe tsaye, tana furta za ta wuce. "Ina zuwa Maryama. Bara na mata rakiya." Baƴuwar ta murmusa ta ce, "Babu komai wallahi Yaya Murja. Ki sha zamanki." "A'a Zaliha. Mu je ko bakin ƙofa ne." Ba ta jima ba ta dawo, tana ba Maryama haƙuri. "Babu komai ai Umma." Bayan ta zauna ta ce, "Ya kika baro su Mama?" "Lafiya ƙalau Umma. Sun ce ma a gaishe ki." "Ina amsawa." Daga nan shiru ya biyo baya. Miƙewa ta yi Umma, ta ce, "Akwai kwaɗon zogale na nan kuwa da na ma Mallam ya yi saura. Bari na kawo miki." Murmushi kawai ta yi Maryama, ta bi Umma da ido har ta ƙarisa cikin kitchen. Sosai take yabawa da kirkin matar. Tana da karamci sosai ba kaɗan ba. Roba ce ta taho riƙe da ita a hannunta, ta rufe da wani ƙaramin plate. A gaban Maryama ta ajjiye, da faraa ta ce, "Ci ki ƙoshi. Idan borkonon bai miki ba sai in kawo miki ki ƙara." Buɗewa ta yi Maryama ta fara ci, sosai kuwa ya mata daɗi, saboda dama ita ɗin maabociyar cin zogale ce. Sai da ta ci kamar rabinsa, sannan ta yi hamdala ga Allah, ta miƙe haɗe da nufar randar gidan, ta wanke hannunta sannan ta sha ruwan ta dawo. A rayuwar Umma, tana son ganin mutum well social, wanda ba ya da jiji da kai ko kuma ƙyamar talaka. Ko ba a faɗa mata ba ta san cewa Maryama suna da rufin asiri a gidansu, amma kuma ga shi babu ƙyama babu komai ta ci abincinsu, ta sha ruwan randarsu. Wasu halayen na Maryama sukan tuno mata da Amrarta, sosai ba kaɗan ba. Girmama na gaba da yawaita fara'a, duka haka Amrah take. Bayan ta zauna Maryama, ta sake yi wa Umma godiya, sanan ta ɗora da faɗin, "Umma dama akwai wata magana da nake son sanar da ke." Gyara zamanta ta yi Umma, ta ce, "Allah ya sa lafiya." Murmushi ta yi Maryama, ta ce, "Lafiya ƙalau Umma. Dama kan maganar Annur ne." "To ina saurarenki." Umma ta faɗa. Bayan ta sauke ajiyar zuciya Maryama, ta ce, "Umma abubuwa da dama sun faru bayan bari na gidan nan. Na shiga cikin rayuwar Annur sosai, na gano munana halayensa da kika faɗa min, har ma sun zarce yadda kike tunani ɗin. Sannan kuma wani katari da aka yi, ƙanwar nan tashi Dr. Islam da kike faɗa min ƴar wulakanci, yaronta Abdul tare suke da ƙanina Muhammad a makaranta, har ta silarsa ma mun ƴulla zumunci da ita. A taƙaice dai, na shiga rayuwarsa Annur tsamo tsamo, na nemi ceto shi daga halin da yake ciki, sai kuma wata matsala ta kunno kai." Shiru ta yi daga nan, tana nazarin ta inda za ta fara sanar da Umma cewa ba shi ne real Annur ba, shi ɗin na ƙarya ne. "Uhm, ina saurarenki Maryama." Maryama ta ci gaba da, "Ta hanyar wata kilakin Annur, na gano cewa ba ainahin Annur ba ne a gidansu." Ido Umma ta ƙwalalo tana kallon Maryama. Ta ma rasa gane inda maganar tata ta dosa. "Mun gano inda Annur ɗin Amrah yake. Cikin halin hauka muka same sa, wadda aka tabbatar mana cewa ya ɗauki kusan tsawon shekaru uku a wannan halin, a garin Maraɗi. Yanzu haka maganar da nake miki Umma, Annur na gidanmu ajje, ana ba shi kulawa." Ta kasa gasgata maganganun Maryama, sai dai kuma tana hango tsantsar gaskiya a cikin ƙwayar idonta. Cikin muryar mamaki ta furta, "Ta ya hakan za ta faru? Me ya sa kuma kamanninsu ɗaya babu bambanci? Kenan su ɗin ƴan biyu ne?" "Abin da har yanzu nake tambayar kaina kenan, na kuma gaza samo amsa. Kawai dai abin da na sani ɗaya ne, shi ne basu da bambanci ko kaɗan. Bambancin kawai shi wannan cikin halin hauka yake. Kuma kullum cikin ambatar sunan Amrah yake, yana furta Amrah yake so. Amrah zai aura. A kai shi inda Amrah." Runtse idanuwanta ta yi Umma. A hankali ta buɗe su, cikin mamaki ta ce, "Na tabbata ba za ki min ƙarya ba Maryama. Na yarda da ke, na kuma yarda cewa wanda kika tsinto ɗin shi ne ainahin Annur, saboda ko bayan haukacewarsa kafin a ce mana ya warke, subbatunsa kullum a kan Amrah ne, yana faɗin ita yake so. Amma da mamaki. Ta ya aka yi hakan ta kasance?" * Ruwa da lemo Mama ta kawo ma Kawu Imrana da kuma Abba. Bayan sun gaisa ne take ce masa, "Daɗa Alhaji tunda ka tafi sai muka ji ka shiru, kamar ma ka manta da kana da dangi a Katsina." Murmushi ya yi bayan ya sauke glass cup daga bakinsa. Ya ce, "Ta ya zan iya mantawa da ku? Kuna raina a kodayaushe. Aiki ne kawai ya sha gabana. Amma yanzu komai ya daidaita, na gama, na kuma dawo gida cikin iyali da dangi." Abba ya murmusa, ya ce, "Hakan ya fi ai. Muna ta fama da kewarka." Sosai suke wasa da dariya da junansu, tamkar Kawu Imrana ba shi ba ne babba. A ƙarshe ya yi gyaran muryarsa, ya ce, "Wata shawara ce na yanke da ni da zuciyata. Cewa zan haɗa yaran nan aure. Ina nufin Ahmad Deedah da kuma ƴata Maryama." Idanuwansu buɗe cike da farin ciki suke dubar Kawu Imrana. Tun Abba bai ce komai ba Mama ta yi saurin faɗin, "Lallai gaskiyar Hausawa ne da suka ce, abin da babba ya hango yaro ko ya hau turmi ba zai taɓa hango shi ba. Da gaske na ji daɗin wannan al'amarin sosai, na kuma tabbata akwai kyakkyawar alaƙa a tsakanin yaran, za su daidaita kansu." Tana kaiwa nan Abba ya ce, "Sau ɗaya wannan batun ya taɓa faɗo min a rai, sai dai kuma na bar wa cikina, sanin halin yaran yanzu, kar su watsa mana ƙasa a ido." Kawu Imrana ya ce, "Kafin na tinkare ku da zancen sai da na yi maganar da Deedah, cikin hikima na nemin jin tsakaninsa da Maryama. Yake faɗa min yadda suke, akwai zumunci sosai a tsakaninsu. Saboda haka ba na ji ko kaɗan za su baɗa mana ƙasa a idanuwa. Addua kawai za mu musu, Allah ya sa wannan haɗin ya zama alkhairi a tsakaninmu baki ɗaya." "Ameen ameen Yaya. Gaskiya ka yi tunani mai kyau. Tunda dai dama yana aikinsa, ai sai maganar aure kawai. Ita ɗin kuma za ta iya ci gaba da karatunta ko a gidansa." Da haka suka miƙe, Abba ya ce zai miyar da shi gida, shi kuma daga nan zai koma Office. Bankwana Mama ta musu, sanann ta dawo ta zauna. Tana jin farin ciki sosai lulluɓe da zuciyarta. *** *To fa! To fa masu karatu! You see ba. Kun ga abin da yake shirin faruwa ko?😱 wai Deedah za a haɗa aure da Maryama, wacce ke da burin zame ma Annur Amrarsa da ya rasa. To ya wannan abu zai kaya? Ko Maryama za ta amince da wannan zaɓin na iyayenta? Idan ta amince ya makomar rayuwar Annur? Tirƙashi! Akwai aiki mai girma.* *Shin akwai wani taimako da Maman Amrah za ta iya yi ma Maryama ta hanyar warwaruwar wannan ƙullin?* *Mun dai ga halin da Sans ya shiga, a wasu shekaru da suka gabata. Shin komawar da zai yi Bama ko zai zame masa alkhairi? Iyayensa sun mutu kuwa? Wane dalili ne ya saka shi dawowa Katsina bayan kuma shi ɗin ɗan Maiduguri ne? Me ya sa halayensa baki ɗaya suka munana, har ya koma halin da yake kai a yanzu?* *Ku ci gaba da bibiyata, sannu a hankali duk za a samu wannan amsoshin. I love y'll Fisabilillah. Kun sani ai.😀* *Kar ku manta, sai kuna yi kuna kankaro mutunci. Yanzu kam abun ba dama, ghosts sun yi yawa. Sannunku kun ji? Babu kunya a karanta a ƙetare kyakkyawar tauraruwar nan mai daɗin dangwalawa.😁* Thanks all Pinky durling💞 RAZ 2 [9/1, 1:39 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 5⃣2⃣ Wattpad: PrincessAmrah *** Tsaye ta miƙe bisa ƙafafuwanta. Fuskarta ba yabo ba fallasa ta fuskanci Umma da faɗin, "Umma zan tafi. Amma don Allah ina buƙatar taimako daga gare ki." Da fara'a Umma ta ce, "Allah sa bai fi ƙarfina ba." Maryama ta furzar da zazzafan iska daga bakinta, a lokaci guda kuma ta sauke ajiyar zuciya, ta ce, "So nake ki ringa zuwa gidanmu akai-akai wurin Annur. Ina tunanin ganinki da zai ringa yi ƙila ya ringa tunowa da wasu abubuwa na Amrah, ta sanadiyyar haka har ƙwalwarsa ta dawo daidai. Da na yi tunanin na ringa kawo shi nan da kaina, sai kuma nake gudun faruwar wani abu; kar wancan Annur ɗin na ƙarya ya aikata wani mummunan abu, duk da yake dai har yanzu ba mu san taƙamai-mai yadda abun nan ya kasance ba." Dafa kafaɗar Maryama ta yi Umma. Ta ce, "Insha Allahu zan ringa zuwa kamar yadda kike da buƙata. Amma a ganina, me zai hana ku miyar da shi gidansu, tare da bayyana duk yadda abin ya kasance? Kamar hakan zai fi wannan ɓoye-ɓoyen ai." Maryama ta ce, "Zan yi hakan Umma. Sai dai lokaci bai yi ba har yanzu. Ko kaɗan ba na so Yaa Noor ya koma gidansu da hauka, saboda ba mu san ƙudirin wancan na ƙaryar ba. Amma kin ga idan ya ji sauƙi, zai iya nemawa kansa kariya, zai kuma iya tabbatarwa iyayensa cewa shi ne ainahin Annur." "Tabbas kuwa kin yi gaskiya Maryama. Allah Ya ba shi lafiya. Ki min kwatance gidanku insha Allahu zan zo gobe." Kwatancen kuwa ta yi ma Umma, sannan ta kama hanyar barin gidan. Da faraa ta shiga gidansu bayan ta yi sallama. A falo ta samu Mama zaune da hijabi a jikinta, da alama sallar azahar ta gama, saboda lokacin har sha biyu ta wuce. "Sannu Maryama. Har an dawo?" "Na dawo Mama." Ta faɗa cikin muryar gajiya haɗe da cire hijabinta. "Umman Amrah ta ce na gaishe ki Mama. Gobe ma za ta zo ta duba Yaa Noor." Mama ta ce, "To Allah Ya kai mu. Ina amsawa. Sai ki nufi sallah ko. Idan kin fito ki kai ma Annur ɗin abincinsa, ki ba shi magani. Ki zo ki ci naki ke ma." "To Mama." Ta furta bayan ta miƙe. Ta nufi ɗakinta. Sai da ta ɗan watsa ruwa sannan ta saka ƙananan kaya ta fito. Abincin na Modu ta zuba masa a plate, sannan ta nufin ɗakin nasa, fuskarta ƙunshe da murmushi. Yana ganinta ya miƙe tsaye, da alamun dama ita yake tsumaye. "Ya Noor sannu da hutawa." Ta faɗa cikin sassanyar muryarta, bayan ta zauna a bakin gado. Bai ce da ita komai ba, kamar yadda dama ba ta yi tsammanin jin wani furuci daga gare shi ba. "To ga abincinka nan. Ka ci sai ka sha magani. Ina zuwa bari in dawo." Ta bar ɗakin, babu jimawa sai ga ta ta dawo hannunta riƙe da wayarta. Samunsa ta yi bai ci komai ba. Hakan ya sa ta ɓata fuskarta, ta saita idanuwanta a cikin nasa. "Me kake nufi na ga ko taɓa abincin ba ka yi ba. Ko wani abu ya faru ne? Akwai abin da kake so Yaa Noor?" Duk ta marairaice fuska, cike da damuwa. Gyaɗa mata kansa ya yi, take ta fara ganin ruwan hawaye a idanuwansa. Nan take jikinta ya ɗauki rawa. Ba ta san me ke damun Modu ba. Yau ga shi yana kuka, wanda tunda ta ɗauko shi yau ce rana ta farko da ya yi kuka. "Yaa Noor na maka laifi ne? Bayan na tafi Mamana ta maka wani abu ne? Ko Abba ne? Please tell me." Runtse idanuwansa ya yi tare da matso wasu ruwan hawayen. Ya sunkuyar da kansa ƙasa. "My God!" Ta dafe kanta, tana jin wani yanayi mai wuyar fassarawa. Ba ta san me yake damunsa ba. "Amrah ta ƙi dawowa gare ni, bayan kuma ta san ba zan iya rayuwa ba tare da ita ba. Me ya sa za ta min haka? Me ya sa za ta min nisa ta ƙi waiwaya ta?" Cike da tausayi ta sauke ajiyar zuciya, cikin kwantar da hankali ta fara masa magana, "Ka daina kukan to ya isa haka. Mun yi waya da Umman Amrah, ta ce min gobe za ta zo..." Bai ko bari ta rufe bakinta ba ya yi caraf ya ce, "Tare da Amrah za su zo? Yeee! Na ji daɗi zan ga Amrata." Ɗan taunar leɓonta ta yi Maryama. Ta ce, "Ai in dai har ba ka daina kukan nan ba to zan hana ta zuwa." Hannuwansa duka biyun ya sa ya ringa shafar hawayensa, yana faɗin, "Na daina. Allah ba zan kuma yin kukan ba." "Yauwa Yayana. To ka ci abincinka. Ko ni kake so na ba ka a baki?" Bai ce mata komai ba ya fara zira abincin a bakinsa, hannu baka hannu ƙwarya. Sai da ta tabbatar ta ba shi magani sannan ta masa sallama ta fita, saboda jin Mama ta ƙwala mata kira, kuma ma akwai abin da take son yi a waya, kukan da ya yi ne ya dakatar da ita. Kusa da Mama ta zauna bayan ta ɗora wayarta a bisa cinya. Ta ce, "Mama ga ni." Tun kafin Mamar tata ta ce komai suka ji sallama. Wata ƙawar Mama ce ta yi sallamar, fuskarta ƙunshe da faraa. Amsa sallamar suka yi a tare, Maryama ta gaishe ta, sannan ta ba su wuri. A bisa gadonta take kwance. Ta kunna datarta, sannan ta shiga website ɗin da suka fara magana da Sandra. Tana shiga ta inbox ɗinta ta ci karo da lambar Dr. Hamdan M. Ramat, sai kuma ta Dr. Aqaaq Saifullahi daga ƙasa. Ta ba ta haƙuri cewa ta ji ta shiru ba ta neme ta ba, ayyuka ne suka sha kanta. Ganin kamar ba ta kusa Dr. Sandra ɗin, ya sa Maryama ta sauka, bayan ta ɗauki lambobin. Ta Aqaaq Saifullahi ta fara nema Call forwaded, hakan ya sa ta latsa ta Dr. Hamdan ɗin. Bugu uku ya ɗauka da sallama ƙunshe a bakinsa, ita ɗin ma haka. Hakan ya sa suka amsa sallamar a tare, Maryama ta gaishe shi cikin girmamawa. Cikin seconds kaɗan ta gano cewa Dr. Hamdan mutumin kirki ne, babu girman kai ko kaɗan a tattare da shi, a yanayin da ya amsa gaisuwarta kawai. "How may I help you?" Ta jiyo muryarsa ya ambata, cikin sassanyar muryarsa mai cike da dattako. "Ahmm...I'm Maryam by name, calling You from Katsina." "Go on..." Ta ji ya ambata, da alama yana wani aiki ne, kasantuwar likitoci dama lokutan kansu ƙalilan ne. "I heard alot about you, from Dr. Sandra. So, I just decided to contact you, am sure you'll help me out of my problems." "Uhm." Ya faɗa yana saurarenta. "My brother is seriouly ill, for a long time. He has a mental problem, or may be a lost of memory, I don't exactly know." "Oh! This is serious. The most important thing is that in gan shi zahiri. Kin ce you are from Katsina right?" "Yes Dr." Ta faɗa cike da girmamawa. "Can you come to Maiduguri?" Ras! Ta ji gabanta ya faɗi. 'Maiduguri?' ta ambata a birnin zuciyarta. A yadda take jin matsaltsalun Borno ne za ta yi fatar kai kanta can? Lallai kuwa akwai damuwa. "Are you with me?" Ta ji ya ambata. Hakan ya sa ta gaggauta faɗin, "Ye...yes Dr." "Ok. The best solution shi ne a kawo shi ɗin, saboda I can't decide anything without seeing the patient. Zan duba schedules nawa, zan ba ki appointment. Ki kira ni by 8pm today." "Thank you very much Dr. I'll call you by Allah's will." Ta kashe kiran. Tana jin yadda gabanta ke faɗuwa. Saboda har ga Allah ita kam tinkarar Borno a ganinta babban siyar da rai ne. Idan ma har ta amince za ta je ɗin, ta tabbata iyayenta ba za su amince mata ba. Miƙewa ta yi jiki babu ƙwari ta jona wayarta caji, sannan ta koma falo wurin Mama. Ta samu har baƙuwar ta tafi, sai Mama kaɗai zaune tana kallon tashar Arewa 24, da suka saka film ɗin Ƴar Duniya. Yanayinta kawai Mama ta karanta ta tabbatar akwai abin da yake damunta. Ba ta damu da sanin ko miye ba, saboda ta fahimci kamar tirsasa sanin damuwarta ne ke haddasa take shirga mata ƙarya. "Maryama albishir kuwa nake so na miki." Kwantar da kanta ta yi a ciyar Mama, ta zame ɗankwalinta da nufin ta mata susar kai. "Ina jin ki Mamana. An dai je a ɗauko Hammad daga School ko? Don ni kam tsoron mitarsa nake." Murmusawa ta yi Mama, ta ce, "Mun yi waya da Abbanku yanzun nan, ya ce ya tura Mallam Ya'u ya ɗauko shi." "Yauwa. Don ni kam tsoron Hammad nake. Rigimarsa yawa gare ta." Murmushi kawai ta yi Mama. Ta ce, "Ɗazu Kawunku ya zo, kin sani ai." "Ehh Mama." Ta faɗa tana jawo tsoron kalabarta guda, tana gyara tufƙarta. "Sun yanke shawarar haɗa ku aure, ke da yayanki Deedah..." Zabura ta yi Maryama haɗe da miƙewa zaune, ta tsura duka idanuwanta a fuskar Mama. Cike da mamakin jin kalamanta. "Me ya faru?" Mama ta faɗa, ita ma tana kallon ƴar tata. "Mama don Allah ki ce min wasa kike ba gaske ba." "Ta ya zan miki wasa a abu mai muhimmanci kamar aure? Hukunci ne daga kawunku ya yanke shi, na kuma tabbata babu abin da zai sa a canza shi." Cikin daƙiƙu kaɗan ruwan hawaye suka gama wanke fuskar Maryama, tamkar an ɗebi ruwa an kwara mata. "Mama me ya sa kawu Imrana zai mana haka? Me ya sa ba zai bar kowa da ƙudirinsa ba? Na tabbata Yaya Deedah na da wacce yake so, yana da wacce yake da ƙudirin aure, kamar yadda ni ma ba ni da ƙudirin aurensa, nake masa irin soyayyar yaya da ƙanwa. Don Allah a bar ni da ƙudirina Mama, a bar ni na fidda gwanina da kaina, wallahi ba na son auren Yaya Deedah." Ta faɗa a jikin Mama, tana kuka sosai tamkar wacce aka ma dukan tsiya, ta ko'ina jikinta karkarwa yake. Me ya sa za a mata haka? Me ya sa ba za a bari ta ƙarisa kyakkyawan aikin da ta ɗauko ba? Don me ya sa ba za a bar ta ta zame ma Annur Amrarsa da ya rasa ba? Sai da suka gama shaƙuwa da Annur ne za a mata wannan zaɓin? Yaushe rabon da a yi auren haɗi? Kamar iyayen yanzu sun waye ai, sun daina yi wa yaransu auren dole, saboda sun fuskanci matsalolin da yake haifarwa. Kuka take mai sauti, mai cike da tashin hankali da neman agaji. Sosai take jin wani irin raɗaɗi da zugi a zuciyarta, tsanar Ahmad Deedah na shiga ta kowanne saƙo da ke cikin zuciyarta. *** Suna daf da shiga garin Bama suka fara ganin tashin hankalin da ke wakana a garin. Da gawarwakin sojoji suka fara cin karo, wanda ya ƙara tsoratar da su. Sojoji duk training ɗin nasu da komai amma a haka aka karkashe su, aka yasar da gawarwakinsu, wato don ma mutane su gani su ƙara tsorata. "Shi kenan na rasu su! Na tabbata an gama da su..." Ya fasa ƙara mai ƙarfi, yana mai fuskantar dreban da duka hankalinshi. "Ka gani ko? Da alama sun cinye garin baki ɗaya. Sun gama da kowa da ke ciki." Dakatawa ya yi da mota dreban. Ya ma rasa yadda zai yi da Sans. Kallonsa yake cike da tausayinsa. Wannan babbar jarrabta ce, mai wuyar hayewa. Tun sadda suka kamo hanyar garin Bama Sans ke ba Dreban labarinsa, da duk abin da ya faru tun farkon kiran da Abbansa ya masa. Kamar da wasa suka ringa jiyo ƙarar mota, da kuma hasken fitilun motocin da suke gabatowa. Hankulansu ne suka tashi. Dukkanin nutsuwarsu ta gushe. A hankali Sans ya buɗe murfin gaban motar, ya shawarci dreban ma da ya ƙoƙarta ficewa cikin hikima, ta yadda ba za a gan shi ba, duk dayake cewa ba su san ko su waye tafe ɗin ba. Daga bayan motar suka ɓoye, maƙalƙale da juna suke, ƙirazansu na duka, duniyarsu na juye musu. Suna jin sadda motar farko ta wuce da ƙara tiiiii! Kamar za ta tashi sama. Ta biyun ce ta ƙoƙarta dakatawa a gefen tasu motar, tare da kashe wutarta. Sunan Allah suke son ambata amma sun neme shi sun rasa. Tashin hankali suke ciki wanda suka gaza tuna kalmar addua ko guda. Fincikarsa ya ji an yi Sans, cikin wannan halin ya kalli matashin da ya finciko shi ɗin. Sanye yake da dark glasses, hannunsa riƙe da bindiga ƙarama, gudan hannun kuma ya shaƙure Sans ɗin da shi, yana kallon cikin idonsa. Kafin ka ce me, wurin ya cike da bataliyar ƴan ta'addan, wanda mafi rinjaye na cikinsu sanye suke da kakin sojoji, da alama mutanen sojojin da suka kashe ne, suka cire kayansu suka miyar a jikinsu. Dariya wani daga cikinsu ya fasa da ƙarfi. Ya kalli Dreba da ya gama tsurewa ganin yadda ake jijjiga Sans. Bai ankara ba ya ji sautin bindiga, an harbi gefen titi da ita. Cikin tsoro da kiɗima ya ce, "Don Allah don Annabi ku min rai, wallahi na tuba, ku yi haƙuri don Allah, ƙaddara ce ta shigo da mu. Kar ku mana komai don Allah." Wani ƙato baƙi-ƙirin mai jajayen idanuwa, fuskarnan tasa ɗaure tamau ya kalli dreban da faɗin, "Ba a magana a duk inda muke. Duk wanda ya yi ta kuwa furucinsa na ƙarshe kenan a duniya. Zan maka uzuri, ka ƙara kalma guda kawai, ko kalimatushshahada ka yi, wata ƙila ka samu rabo a can." Matasan da za su kai kimanin biyar suka tulle da dariya, banda wanda ya yi maganar. Bakinsa rawa yake dreban, baki ɗaya jijiya da jininsa yake jin suna dakatawa da aiki, sanadiyyar harsashin bindiga da ya ji a saitin zuciyarsa. "Allah, Allah!" Su ne kalmominsa na ƙarshe, sanann rayuwarsa ta fita. Ƙara ya saki da ƙarfi sosai Sans. So yake shi ɗin ma su kashe shi. Bai ga amfanin rayuwarsa a daidai wannan lokacin ba. "Ƙarshenku ba zai yi kyau ba. Sai Allah ya saka ma duk wanda kuka zalunta. Ina kuka kai min iyaye da kuma ƙanwata? Ku faɗa min ina suke? Ina Aunty take? Ta samu abinci ta ci? Yamaira ƙanwata tana ina? Ina Abbuna?" Kamar zautacce yake sako wannan zantukan, yana ƙoƙarin ƙwace kansa daga hannun wancan matashin, da dukka ƙarfin da ya masa saura. Wata irin muguwar jifa matashin ya yi da Sans, sai bisa wani ƙaton dutse ya buga kansa da ƙarfi. A take jini ya fara malala daga kan nasa, wanda hakan ya tabbatar musu da cewa ba ya raye. Barin wurin suka yi su dukansu, amma wancan ɗayan bai tafi ba sai da ya ma Sans harbi biyu a ƙafarsa ta dama, sannan ya masa ɗaya a ƙafar haggu, duk da cewa a tunaninsa ba ya raye, kawai dai yana son ya ƙarisa huce takaicinsa ne. A nan suka tafi suka bar Sans da ke kwance ba ya numfashi, da kuma dreban da tun ɗazu ya mutu. *** *This page is too short, I know. A yi haƙuri da zuwansa haka, na so ya zarce, amma Allah bai nufa ba, kuma ina son yin posting ɗin yau, saboda farin cikin wasu bayin Allah. Kun san ko su waye? Aunty Maijidda Musa is among. Basman mai sanyinta ba zan gajiya da ambatarki a pages na book ɗin nan ba. Kina raina, ina kuma jin daɗin comments ɗin ki. Habibaty Queeny, Queen miemie ke ma, kina cikin wanda za na gaisar. Iya wuya ana tare, ina yin ku, ina ƙaunarku fisabilillah🤝* *Gaskiya dai wattpad ya kamata a ce an koya mana yadda za mu ringa gano Ghosties, mu ringa ganin duk wani mai karanta mana post amma ya kasa kankaro mutunci😎 sai iya ƙwalala ido a karanta, ana jin daɗin abun amma baki ya gaza furta comment, hannu ya gagara dangwala tauraro. Kun ji ni ai ba? Sannunku kun ji.😏* *Masu votes duk ina gani, ina kuma tsananin jin daɗi wallahi. Ku kuke daɗa ƙarfafa mini guiwa, har nake yin update a kan lokaci😘😍* Thanks all Pinky durling💞 RAZ 2 [9/2, 3:58 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 5⃣3⃣ Wattpad: PrincessAmrah Kimanin awanni goma sha takwas ya ɗauka a halin da yake ciki. Domin kuwa tun sadda ƴan ta'addan suka masa wannan ta'asar ya yi mummnar suma, wacce in da a gaban wasu ya yi ta, tuni an binne shi ma. Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke. Abubuwan da suka wakana ne suka hau faɗo masa. Yadda ya ringa sako magana tamkar ba ya cikin hayyacinsa, da kuma sadda aka jefa shi jikin dutse. Raɗaɗi yake ji tun daga fatar kansa har izuwa cikin kwanyarsa. Ƙafarsa, ciwo take masa mai tsanani, haka ɗayar ƙafar ma, sai dai kuma ba ta kai ɗayar azaba ba. Wani irin ƙunci yake ji Sans, a zuciyarsa yake fatar mutuwa ta zo masa. Mutuwa ta zo ta ɗauke shi, zai fi jin daɗin hakan, fiye da rayuwar da yake da ita a wannan lokacin. A ce yau shi ne ya wayi gari babu Abbaunsa, babu mahaifiyarsa, babu kuma tilon ƙanwarsa da ya fi ji da ita a duk duniyarsa. Yunƙurin tashi zaune ya yi amma ya kasa. Jikin nasa ya masa tsami sosai. Ga ƙishi da yunwa da suke addabarsa. Kuma babu ko halittar dabba da ke gicci a dajin bare ya sa ran ganin bil-Adama. Kusan shida na yamma kenan, rana ta fara ƙoƙarin faɗuwa. Daga inda yake kwance ya ɗago kanshi ya kallo Dreban nan kwance ƙasa babu ko alamar numfashi a tattare da shi. Numfashi ya saki mai ƙarfi, haɗe da sakin kuwwa wacce ta karaɗe dajin, har ana jin echo sound na dawowa, duk da kuwa open place ne. "Oh Allah! Save me ya Allah!" Ya runtse idanuwansa. Zafafan hawaye na fitowa daga cikinsu, suna gangarowa bisa kumatunsa. A nan inda yake ya kwana, kashi da fitsari duk a nan ya yi su. Ba ya iya ko tashi zaune, bare kuma mikƙwa, har ya yi tsammanin guduwa ya bar wurin. Da asubar fari ya farka. Mutane ya ji a kusa da shi, yana jin saukar numfashinsu. "Kar ka ji tsoro, mu ba azzalumai ba ne." Ya ji saukar maganar wani matashi a kunnuwansa. Buɗe idanuwansa ya yi, ya tsura masa su, tare da taunar duka laɓɓansa. "Mun zo wucewa ne muka hangi mota, to mu kuma dama ta mu ta tsaya babu mai, shi ne muka yanke shawarar matsowa nan, koda taimakon da za mu samu. To kuma sai muka ga gawar wancan bawan Allah, ga kuma kai a nan, cikin wani hali. Jin alamun kana numfashi ya sa muka yanke shawarar taimaka maka. Wallahi mu ba macuta ba ne." "Ta ya zan yarda cewa ku ba macuta ba ne? Me zai shigar da ku cikin garin da ƴan ta'adda suka gama mamayewa, suka cinye shi baki ɗaya?" "Ba shiga za mu yi ba, hangi motarmu ga ta can, fita za mu yi. Muna cikin garin sadda yamutsin ya fara, ɓoye a wani wuri, Allah kuma ya taimaka mana babu wanda ya kama mu. Jin tsit ya sa muka yanke hukuncin fitowa, komai ta fanjama fanjam! Ga shi dai kuma Allah ya taimaka mana mun fito ba mu haɗu da wani hargitsi ba, amma kuma man motar ya ƙare. Ka ba mu damar tamakonka bawan Allah." Kai kawai ya jinjina musu alamar ya yarda. Kama shi suka yi su uku suka kai motarsu. Sannan da dabara suka ringa tsotsar man taxi ɗin suna zubawa a tasu. Ƙarfe tara na safe ta musu a cikin garin Maiduguri. Kai tsaye asibiti suka nufa da shi, take aka karɓe shi Emergency  Likitoci suka hau kansa, domin ba shi taimakon gaggawa. *** Wani irin yammaci ne ta yi mai cike da ƙunci da takaici. Rayuwarta take tunani, da kuma makomar Annur. Idan har ta bari ta auri Deedah, ta tabbata ba za ta taɓa ci gaba da taimakon da ta ɗauko ba. Ta sani, Ahmad Deedah mutum ne mai tsananin kishi, wanda ba ma ga budurwarsa kawai ba, har ga ƴan uwansa kishi gare shi. Yana da ƙani mai suna Khalil, haushi yake ji ya ga yadda Maryama ke kula da Khalil, ko da kuwa gaishe shi kawai ta ce ya yi. Mugun kishi ya raba shi da budurwarsa Labibah. Mace mai tarbiyya da girmama na gaba da ita. Ta san darajar duk wani dangin Deedah. Sai da har iyaye suka shiga zancen, amma kawai mistakenly ya gan ta tsaye da namiji a school, zuciya ta ɗibe shi, har ya gaura mata mari. Wannan marin ne ya yi silar rabuwarsu, yanzu haka ma ta yi aurenta har da yaro guda ɗaya. To a haka ne za ta iya auren Deedah? Ina, ba za ta iya ba. Dole ma ta samu Abba da maganar, wala'Allah zai suarare ta, ya kuma dubi lamarinta. A bisa tafukan ƙafafuwanta ta miƙe. Ji take tamkar duga-duganta za su tsattsarge tsabar gaza ɗaukar gangar jikinta da suka yi. Jikinta ya yi sanyi ƙwarai, ta kowacce gaɓa da ke jikin nata karkarwa take. Cikin sanyin jiki ta runtse idanuwanta duka biyu, tana mai tsananin jin zafin duniyarta. Lallai rayuwa ta juye mata; daga farin ciki zuwa baƙin ciki. Zuciyarta ta dafe da hannunta na dama, ta ji yanda take duka da sauri da sauri, kamar ma ba daidai take tafiya ba. Gyaɗa kanta ta yi bayan ta buɗe idanuwan, cikin rawar murya ta furta, "Ba zan iya ba. Wallahi ba zan iya auren Yaya Deedah ba. Annur nake so, shi nake da muradin aure, koda hankali ko babu shi." Ta faɗa bisa gadon ta ɗora fuskarta a bisa pillow, ruwan hawayen na sauka a bisa kyakkyawar rigar pillow ɗinta pink colour. Sallar magrib ake kira, dama dalilin miƙewar da ta yi kenan, amma ta kasa controlling temper ɗinta. Kamar kar a fara mata maganar auren Deedah, ta ƙara jin bunƙasuwar soyayyar Annur a cikin zuciyarta. Ba tausayin Annur kaɗai take ba, sai yanzu ta ƙara tabbatar da hakan, har da soyayyarsa, wacce ke ɗawainiya da dukkan jiki da ruhinta. Sake runtse idanuwanta ta yi, take hango murmushinsa, kalaminsa, da yadda yake ɗora yalwatattu idanuwansa a fuskarta. Annur bai da matsala ko kaɗan, ta sani. Kyakkyawa ne managarci, cikar zati da tausasshe murmushi. Damuwarsa kawai halin da yake ciki, wanda take sa ran taimakonshi duk tsiya duk rintsi. Daurewa ta yi ta miƙe ta nufi ban-ɗaki, alwalla ta ɗauro sannan ta ƙoƙarta saita kanta, ta kabbarta sallar magrib. A bisa sallayar take zaune tana adhkar, tana ƙara sanar wa Allah damuwarta, tare da rokonSa mafita ta alkhairi. Sai da ta yi sallar isha sannan ta sauka daga bisa sallayar. Ta faɗa kan gadonta, tana tunanin kiran Dr. Hamdan. Ba ta jin za ta iya magana da shi a wannan mood ɗin, to ma me za ta faɗa masa? Idan har ya ba ta appointment ɗin, yaushe ne za ta je Maiduguri ta kai masa Annur, bayan kuma ga zaɓin da iyayenta suka mata? Saurin kwaɓar bakinta ta yi, jin yana neman tabbatar mata da zaɓin na iyayenta. Ba fa za ta auri Deedah ba, haka take faɗi a ƙuntatacciyar zuciyarta, mai cike da ƙunci, tashin hankali da kuma fargaba. Muryar Muhammad ta ji a saitin kunnuwanta yana faɗin, "Yaya Maryama tun ɗazu nake miki sallama, ban san me ya sa ba ki amsa ba." Fuskarta a tamke take kallonshi, ta gagara furta masa komai. "Abba ne yake kiranki dama." Ya faɗa cikin halin ko'inkula, haɗe da barin ɗakin da gudunsa. Shi kenan, ta faru ta ƙare, an ma mai dame ɗaya sata! Ta tabbata maganar auren Deedah ce zai mata, dama Mama ta ce idan ya dawo zai tinkare ta da maganar da kansa, kuma idan har tana son farin cikinsu, to kar ta nuna ba ta so. Wayarta ta jona jikin caji, sannan ta miƙe tsaye, dama ba ta cire hijabin jikinta ba kawai ta fice, ta nufi ɗakin Abbanta. *** Ƙirjinsa ya dafe da dukka hannuwansa, tari yake iya ƙarfinsa, mai fitowa haɗe da jini. Tun yana yi bai galabaita ba, har abun nasa ya ci tura, ya galabaita sosai. Sans (Fake Annur) da shigowarsa gidan kenan ya biya ta ɓangaren Mami ya gaishe ta, sannan ya wuto zuwa ɗakin Bobby. A halin da ya same shi ne ya matuƙar tayar da hankalinsa. Cikin razana ya isa ga Farouk, ya ringa faɗin, "Guy me ya faru? Jikin ne? Me ya sa ba ka je ka sanar ma su Mami ba? Tana can tana cewa ƙila ma ba ka gidan. Guy dole su Mami su san tsanantar da abun nan ya yi. Dole ne su san me yake damunka, da kuma silar cutar baki ɗaya. Wata ƙila su fidda kai waje. Amma zama haka ai ba zai yiwu ba." Duk wannan surutan da Sans ke yi ma Farouk bai san yana yin su ba. Saboda tuni ya sume, yana sauke numfashi a sannu a sannu. Fahimtar hakan da Sans ya yi ya sa shi fita da sauri, har yana kai wa bango karo. A gujensa ya isa inda Mami, yana famar shessheƙa, hawaye na zirara daga idanuwansa. Cikin kiɗima Mami ta ware idanuwanta ga Sans, bakinta na son yin magana amma ta gaza furta komai. Zuciyarta na ƙissima mata lallai akwai abin da yake faruwa. Dadyn Farouk da ke ƙoƙarin fitowa daga ɗakinsa ne ya ga abin da ke faruwa, cikin tashin hankali ya ce, "Annur me yake faruwa?" Muryarsa rawa take sosai, da ƙyar ake iya gane abin da yake faɗi, ya ce, "Dady...ga...Guy...uhm, Farouk can kwance, jikinsa ya yi tsanani sosai..." Tun bai rufe baki ba Dady da Mami suka haɗa bakunansa wurin ambatar sunan Allah, haɗe da bin bayan Sans, suka nufi ɗakin Bobby. A yadda Sans ya bar shi haka suka same shi, light blue shirt ɗin da ke jikinsa ta yi kaca-kaca da jini, ya yi kwanciyar ruf da ciki, saboda galabaitar da ya yi. "Umar Farouk!" Dadyn nasa ya faɗa, yana mai jijjiƙa jikinsa. "Umar Farouk kar ka tafi ka bar ni, don Allah kar ka mutu, idan ka tafi ban san me zan faɗawa mahaliccina ba, na gaza cika alƙawarin Yayana da na yi, ga gaza riƙe amana..." Kuka sosai yake yi Dady a wannan gaɓar, yana mai gyaɗa kansa, cike da tausayin Bobby. "A kai shi asibiti Alhaji, ba kuka za mu tasa shi gaba mu yi ba." Mami ta faɗa. Cikin kuka Dady ya ce da ita ta je part ɗinsu ta ɗauko mukullin mota, kafin nan su kuma sun cicciɓe shi zuwa bakin motar. Hakan ne kuwa ya kasance. Bayan sun kai shi mota Sans ya tuka motar, sai Mami a gaba, Dady kuma bayan motar ya ɗora kan Farouk ɗin a bisa cinyarsa, yana kuka sosai na tashin hankali. Me ya sa ya kasa tarbiyyantar da amanarsa? Farouk amanar Alhaji Usman Sardauna ne. Amma me, ya kasa ba shi ingantacciyar tarbiyya. Ya kasa cika alƙawarin da yayansa ya bar masa. Da haka suka isa Alheri Clinic, wanda shi ne asibitin kuɗi mafi kusa da gidansu. A gaggauce Sans ya faka motar, ya fito da gudunsa ya shiga asibitin, ya sanar cewa a zo da gado ko kuma keke, ga patient nan uncouncious. Da gado aka zo aka ɗora Bobby, aka shiga da shi Emergency. Zazzaune suke su duka ukun, kuka suke sosai, banda Sans da ya rafka tagumi, yana zancen zuci, saboda zuciyar tasa ma har ta bushe da zubda ƙwallan. Tunanin rayuwa kawai yake; duniya ta juya musu baya. Ashe dai haka duniya take? Lallai budurwar wawa. Duniya makaranta, wanda bai zo cikinta ba ma jiransa take. Munanan halayen da suka kasance suna aikatawa kawai yake tunani; mugun shaye-shayensu da neman mata. Hannunsa ya ɗora a ka, yana mai gyaɗa kansa. A zuciyarsa yana fatan kar Bobby ya mutu, kar ya tafi a haka ba tare da ya samu rabauta ba. Ya tabbata idan har ya mutu bai tuba ba, akwai damuwa mai girma. Ya sani, ya san hukuncin abubuwan da suka kasance suna aikatawa, saboda shi ɗin mai ilimi ne, duk wannan abubuwan sai dai ya sanar ma wasu. Amma me ya sa bai yi amfani da su ba? Me ya sa ya kasa zama mutumin kirki kamar yadda iyayensa suka ba shi tarbiyya? Son zuciya. Ya samu wannan amsar daga wani ɓare na zuciyarsa. Har kusan ƙarfe sha biyu na dare amma ba a fito da Bobby daga Emergency ba, in short, ba ma su ji wani bayani daga gare shi ba. Jugum-jugum kawai suka yi, babu mai faɗin komai, sai zallar tashin hankali a tattare da su. Wayarsa ce ta yi ƙara Sans. Ya zaro daga aljihunsa, yana gani biji-biji, da ƙyar ya iya gano sunan Momy ne maƙale a screen ɗin wayar. Cikin saɓular jiki ya ɗaga kiran, yana mai kanga ta a kunnensa. "Annur lafiya ba ka dawo gida ba har yanzu? Na faɗa maka za mu yi magana amma tun ɗazu nake zarya zuwa ɗakinka ba ka dawo ba. Wannan ƙawar tawa da muka fara maganarta a waya, tana son a ƙera mata kits ɗin nan, kuma sai kirana take, wai kar lokaci ya ƙure..." Sassarfar kukan da ta jiyo Sans na yi ne ya sa ta dakatawa ba tare da ta kai aya ba. "Me ya faru da kai?" Momy ta furta cike da tashin hankali. "Ga ni a asibiti Momy...Farouk Sardauna ne ba lafiya..." "Inna lillahi wa innaa ilaihi raji'un! Me ya same shi? Ko tarin da ka faɗa min yana yi ɗin ne?" Sai yanzu kuka mai ƙarfi ya samu nasarar kufce masa, wanda har sai da hankalin ƴan reception ɗin ya dawo gare shi. "Shi ne Momy. Shi ne ya galabaitar da shi sosai. Yanzu haka tun ɗazu an shiga da shi, ba mu ji wani labari mai daɗi ba." "Subhanallahi! Allah ya ba shi lafiya. Wace asibitin kuke?" Ta tambaye shi cikin zallar tashin hankali. "Muna Alheri Clinic ne Momy." "To bari na ma Dadyn naku magana, ga mu nan zuwa yanzu insha Allah." "To sai kun zo Momy." Ya furta haɗe da tsinke wayar. Minti talatin bayan gama wayar Sans da Momy wata nurse ta zo, cewa za su iya shigowa ɗakin yanzu, likita ya gama duba shi. Da sauri suka mimmiƙe haɗe da nufar Emergency room, gado na biyu suka hango Bobby kwance, an saka masa Oxygen, ga kuma drip an maƙala masa. Idanuwansa a buɗe suke kyam, yana zuba musu su, ya kalli wannan sannan ya kalli wannan ruwan hawaye ya fito. Sannu kawai suke masa, Dady na faɗin, "Ka yafe min Farouk, ni ne silar komai. Dr. Ya faɗa min Smoking ne silar ciwonka, wanda kuma duk ni na jawo. Ni na gaza baka tarbiyyar kirki, tun kana ɗan shekara goma sha huɗu ka fara shaye-shaye, kuma ban iya ɗaukar matakin shiryar da kai ba, duk da yake cewa Allah Shi ke da shiriya, amma mu ma muna iya zama sila. Allah Ya tashi kafaɗunka Umar Farouk. Allah Ya ba ka lafiya ka ji?" Ya damƙe hannunsa na dama, yana bin sa da idanuwa. Da tambaya su Momy suka iso ɗakin, su kansu cike suke da tashin hankali. Oxygen ɗin da suka ga an maƙala masa ne ya ƙarisa tayar da hankulansu. Ashe dai ciwon har ya tsananta haka. Sama-sama suka gaggaisa, Dadyn Annur da Dadyn Bobby suka gaisa, ya masa ya mai jiki. Haɗa ido Farouk Sardauna ya yi da Dadyn Annur, ya ɗan runtse idanuwansa, sannan ya furzo wasu zafafan hawaye, wanda shi kaɗai ya san raɗaɗinsu. Ganin haka ya sa Dadyn Annur kama hannun Bobby gam ya riƙe, yana tofa mishi addu'o'i. "Nas'alullahul-Azeem, Rabbul-arshil-Azeem, an Yashfiyaka." Ya tofa masa ƙafa bakwai, sannan ya tofa masa "La ba'sa ɗahuran insha Allah!" Ƙafa ɗaya. Yana ƙoƙarin zare hannunsa daga na Bobby ya ji ya riƙe shi gam! Ba ya so ya zare hannun nashi. Wata irin nutsuwa yake ji tana sauka mishi. Ko kaɗan ba ya so Dadyn Annur ya cire hannunshi daga cikin nashi, shi kaɗai ya san daɗin da yake ji. So yake ya yi magana, ya tona asirin ɓoyayyen ƙullin da suka tona rami suka binne, amma ina, abu ya faskara, ya kasa magana, ba ma zai iya ba. Tunda yake a rayuwarsa bai taɓa riƙe hannun wani bawan Allah ya samu irin wannan nutsuwar ba sai yau. Me ya sa? Bai samu wannan amsar ba ne Malukul-mauti ya zo. Mala'ika Azara'eelu, mai yanke ƙauna, mai raba mutum da mutane, mai kawo ƙarshen zaman mutum da duniyarsa. Tsayuwar numfashinsa ta yi daidai da tsayuwar ƙwayar idonsa, haɗe da sauke wani nannauyar ajiyar zuciya, wanda duk sai da suka ji shi, hatta likitan da ke ƙoƙarin shigowa daga bakin ƙofa sai da ya ji numfashin. Zuwanshi ne ya tabbatar musu cewa ba ya numfashi, tashi ta zo ƙarshe, mutuwa ta zo! *** *My pipu how y'all? Its been a while ban saka wata kuka ba ko? I know, yanzu kam wasu sun koka, ba wai don littafin kawai ba, a'a, tsoron tasu mutuwar. Dole fa za ta zo mana, duk daren daɗewa. Me muka tanadar mata? Shin mun shirya tarbarta? Ko ba mu shirya ba dole za ta zo, ayyukanmu na gari ne kawai za su zame mana garkuwa daga azabar ƙabari. Allah Ya sa mu cika da imani.😫* *To jama'a! Me kuke hasashe cikin wannan riƙon da Bobby ya ma Dadyn Annur? Kodai kawai yana son tona asirin Sans ne? Ko kuwa dai akwai wata ƙullaliyar da babu wanda ya sani? Alƙalamin marubuciya Amrah ne kawai zai iya warware mana komai.* *Ina kuke masu mutunci? Ina nufin masu kankaro mutunci, tahm😀 don ku kawai nake posting kullum yanzu, da kuma wasu daga cikin ƴan watsapp masu yawaita comment a kan ANS. Duk ina yin ku sosai kuma ina ƙaunarku fisabilillah. Masu mutunci a ci gaba da kankaro mutunci🤣* Thanks All Pinky durling💞 RAZ 2 [9/3, 1:47 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 5⃣4⃣ Wattpad: Princess Amrah This page is in your honour, Hafsy Gusau. Thanks alot for the care nd concern. Amrah loves you so very much, fisabilillah. *** Hannuwansa duka biyu ya ɗora a ka, kuka yake son yi, amma tashin hankali bai bar shi fasa shi ba. Shin da gaske ne abin da kunnuwansa suka jiye masa? Da gaske Farouk Sardauna ya tafi ya bar shi? Gyaɗa kansa yake, duniyarsa mai cike da ƙunci na riya masa ƙarya ne, Farouk bai mutu ba. Cikin wata irin murya, ya ɗaga sautinshi, ya ce, "Bai mutu ba! Ga shi nan yana motsi. Wallahi Farouk ba zai tafi ya bar ni ba." Sai a sannan hawayen ƙunci suka fara saukar masa. Yana kallon sadda likita ya jawo marufi ya rufe Bobby da shi. Jiki a sanyaye ya dafa kafaɗar Sans, ya ce, "Take heart ka ji? Mutuwa is real, na san ka sani. Kai ɗin ma za ta zo gare ka, ko yanzu ko ba yanzu ba. Ka ɗau haƙuri. Pray for him, ita ya fi buƙata a daidai wannan lokacin. Am very sorry. Sai a nufi ɗaukar gawarsa, idan kuma a nan za ku bar shi ya kwana har safe to." Dadyn Annur ne cikin ƙarfin hali ya ce za su tafi da shi yanzu. A cikin daren suka tafi da gawar Bobby, ta kiran waya da kuma text messages aka ringa sanar da mutane, ƴan uwa da abokan arziƙi. Sans kam tamkar zautacce haka ya koma. Ya yi zaune gaban gawar, shi bai masa addua ba, bai kuma matsa daga gare ta ba. Rayuwa kawai yake tunani. Ya tsura ma gawar idanuwa. Ƙarfe goma na safe aka yi jana'izar Bobby, aka kai shi tabbataccen gidansa, inda kowa sai ya kwanta a cikinsa, komai matsayi da ikon mutum, dole sai ya kwanta a ƙabari. Ko kaɗan wani mulkinka ko kuma muƙaminka ba zai sa a ƙara ko taƙi ɗaya na girman ƙabarin ba. Kamar yadda aka ma talaka haka za a ma mai kuɗi. Ka saba kwana a bisa lallausan gado da katifa, amma sai ka ji ka kwance, inda ko juyi ba za ka iya ba. Allah ka sa mu cika da imani, mu yi kyakkyawan ƙarshe. Sans aka bari ƙarshe bakin ƙabarin Bobby. Cikin sassarfar murya yake faɗin, "Haka mutuwa za ta min? Mutuwa me ya sa za ki tafi da Farouk? Me ya sa za ki tafi da abokina ba tare da kin bar shi ya nadama ba? Allah Ka gafartawa Farouk. Allah ka haskaka makwancinsa. Allah ka yalwata wurin kwanciyarsa. Ya Allah ka gafartawa Farouk kura-kuransa, ɓoyayyu da sanannu..." Kuka sosai ya ci ƙarfinsa. Da ƙyar ya iya miƙewa a bisa tafukan ƙafarsa, ya taka ya bar wurin. Har ya yi nisa bai daina waigen ƙabarin Bobby ba. Bai daina ji kamar mafarki yake ba. Ina ma dai a ce mafarkin ne, zai farka komai tsawonsa. Sai da aka masa nisa sosai, mota guda kawai ke wurin, wadda dadyn Farouk ɗin yake cikinta, da wasu daga cikin abokansa. Cikin motar ya shiga, suka kama hanyar gida. Manya-manyan tabarmu ne aka shimfiɗa ƙarƙashin rumfuna, wanda mutane ke zaune rinkis, suna amsar gaisuwa. Daga jikin bango Sans yake, ya haɗa kai da guiwa, yana jin wasu sabbin hawaye na zo masa. Ba komai ke ƙara tunzura zuciyarsa cikin ƙuncin rashin Bobby ba illa kalaman Dadyn Farouk ɗin, da yake faɗin, "Allahu akbar! Allah mai iko! Allah mai girma da buwaya. Umar Farouk lokaci ya yi, lokacin tafiya ta yi. Yau dai ka bi mariƙinka na ainahi, ka tarar da shi. Wanda sam! Bai taɓa nuna gajiyawa a gare ka ba, duk da kasantuwarka ɗan tsuntuwa a gare shi. Ya damƙa min amanarka, tare da neman alfarmar kar duniya ta taɓa sanin ba ni ne asalin mahaifinsa ba. Allah Ya rahamce ka Farouk. Allah Ya sada ka da dukkan rahamarSa. Allah Ya yafe maka kura-kuranka." Shi kanshi Dadyn Farouk ɗin kuka yake. Zuciyarsa na masa tuƙuƙi, ya dafe kanshi da ɗayan hannunsa. Bayyanannen kuka Sans ke yi, mai cike da nadama da da na sani. Me ya hana su zama mutanen kirki? Me ya sa a lokacin da Bobby ya fara ƙoƙarin ɗora shi a turbar banza, bai fahimtar da shi gaskiya ba? Bai faɗa masa babu kyau maye ba? Cikin wannan halin ne suke amsar gaisuwar. A duk sadda wani zai tambaye shi ya haƙuri? Lokacin ne kuka ke ƙara zo masa. Zuciyarsa ke ƙara azabtuwa da rashin babban amininsa, mai share masa hawaye a duk sadda zai shiga cikin damuwa. Ya sani, ya san cewa ba zai taɓa samun madadin Farouk ba. Ba zai taɓa samun mutumin da zai zame masa tamkar Farouk Sardauna ba. *** A bisa sofa yake zaune Abba. Mug ne a hannunsa wanda yake maƙale da hoton Maryama na sauka. Dama kuma tadarsa ce, duk dare sai ya sha ruwan lipton kafin ya kwanta. Zaman dirshan ta yi a gabansa, tana ƙoƙarin haɗiye sabon kukan da ke niyyar kufce mata. "Barka da dawowa Abba." Ta yaƙi zazzafar zuciyarta wurin tsamo wannan maganar a dunƙule, ta furzo ta waje. "Yauwa Sarauniyar Mata. Tun ɗazu ƴar Baba ba ta zo ta ma Baba barka da zuwa ba. Ko karatu ake ne?" Kanta ta sadda ƙasa, ta ce, "Ehh Abba. Ban ma ji shigowarka ba." "To babu komai ai haka ake so. Ya kamata ma dai ki koma makaranta haka nan, kusan satinki biyu rabon da ki je fa. Ko har yanzu ba a darasin sosai ne?" "Abba mun yi covering ne, exam za mu fara next week." Ta faɗa, har yanzu ba ta ɗago kanta ba. Wanda duk ta sanadin ta tsaya ta kula da Modu ne ta daina zuwa, da gaske sun yi covering ɗin, amma da babu Modu, da za ta ringa zuwa, saboda shiga Libry yin karatu. Bayan ya ajje mug ɗin bisa side drawer, ya ɗora idanuwansa ga Maryama, haɗe da maida dukkan hankalinshi gare ta. "Wata shawara ce Yaya Imrana ya yanke..." Ras! Ta ji gabanta ya faɗi. Ji take tamkar ta ɗora hannuwanta a ka ta kurma ihu. "Cewa za a haɗa ku aure da Babana Ahmad, tunda dai har yanzu bai tsaida mata ba, ke ma kuma ba ki tsaida miji ba. Na tabbata za ku ji daɗin wannan haɗin, koda a gaba ne za ku gode mana." Kukan nata bai iya ɓoyuwa ba, dole ya bayyana. Shessheƙa take ƙasa-ƙasa, ta dafe goshinta da hannun hagunta. Hakan ya tabbatar ma Abbanta cewa zaɓin bai mata ba. Cikin kiɗima mahaifinta ya ce, "Maryama me kike ma kuka? Kar dai ki ce min haɗin ne bai miki ba." Kanta ta ɗaga bayan ta ɗago da fuskarta ta dube shi. Ta kuma sunkuyar da kanta a karo na biyu, kukan nata na daɗa yin ƙarfi. "Don girman Allah Maryama kar ki baɗa min ƙasa a idanuwana. Yaya Imrana mutum ne mai halacci, wanda ya min abin da har in kwanta damata ba zan taɓa mantawa da shi ba. Ya kyautata min, ya riƙe ni da amana a matsayina na ƙaninshi, da iyayemu suka mutu suka bar mu mu biyu kacal, bayan duk danginsu sun guje mu. A lokacin da nake karatu Yaya Imrana ya hana kansa ci da sha, don ganin kawai ya biya min kuɗin makaranta. Akwai lokacin da shekara ta zagayo, shi kuma ya gama UDUS, yana fama da babu, saboda wahala da ɗawainiyar project. Har aka kusa rufe portal ban biya kuɗin makaranta ba. Hakan ya saka shi shiga tsananin damuwa. Ya fara buga can buga nan, don ganin na tsira, na ci gaba da karatuna. Wallahi Maryama har dako Yaya Imrana ya yi, don kawai ya biya min kuɗin karatuna. Tuƙin baro ya yi shi, in taƙaice miki zancen, a wahalce, ni da zai biyama ɗin ma ban wahalar da ya sha ba, ya samu da ƙyar ya biya min wannan kuɗin. Ci da sha da suturata duk a kansa take, saboda shi ya fi ni zafin nema, ya iya aikin ƙarfi sosai, ni kuma ina da laziness. Daidai da auren mahaifiyarki ga ta nan zaune da ranta, Yaya Imrana ya min. Ban san duk wata wahalar neman aure ba, saboda a lokacin har ya fara aikinsa, kuma yana ɗan kasuwanci bakin gwargwado. Maryama da me zan iya saka ma Yaya Imrana? Shin kina tunanin zan iya tinkararsa da zancen wai ba kya son ɗan da ya haifa da cikinsa? Impossible! Wallahi ba ki isa ba! Ba zan iya wannan butulcin ba." Ya ƙarisa wannan maganar da miƙewa tsaye, ya fara jeka-ka-dawo a farfajiyar ɗakin. Sosai kukan da take yi ya tsananta. Wai yanzu da gaske Deedah ake son aura mata? Kar fa abin da take ga kamar ba zai yiwu ba ya yiwu. Ya za ta yi da Annur? "Alhaji a yi haƙuri. Insha Allahu Maryama ba za ta taɓa ba mu kunya ba. Za ta amince da auren Ahmad." "Ko ta amince ko kar ta amince dole a ɗaura wallahi. Yarinya ƙarama kamar Maryam ba ta isa ta saka ni jin kunya ba. Wato a haka kike son ki yita zama babu aure ko? To ba ki isa ba! Aure babu fashi, kuma cikin kwanakin nan. Tashi ki fice min da gani!" A guje ta bar ɗakin ta nufi nata. Muhammad ma bin bayanta ya yi, yana kallon yadda ta faɗa bisa gadon da ƙarfi, tana yin kuka mai sauti. "Am sorry Yaya Maryama. Abba is so angry. Ki bari har ya huce, am very sure zai saurare ki." Ɗago rinannun idanuwanta ta yi ta kalli Muhammad. "Har yaushe kuma Hammad? Rantsuwa fa Abba ya yi. Tunda nake da shi ban taɓa ganinshi a cikin yanayin damuwa ko kuma ɓacin rai irin haka ba, sai yau. Ka sani, Mama ita ce ma mai zafin rai, amma Abba ba ya ɓacin rai, ko ɓata masa rai aka yi yana da wuya ya nunar. Tunda har ka ga haka kuwa, na tabbata ba zai taɓa juyuwa ba. Mama ta taɓa bani wani labari, cewa duk yadda muke ganin Abba da sauƙin kai da sauƙin hali, akwai lokutan da idan ya yi fushi ba ya da sauƙi. Babu kuma wanda ya isa ya sauko da shi sai Kawu Imrana..." "To kawai ki haɗa shi da kawu Imranan." Muhammad ya dakatar da ita da faɗin haka. Murmushin takaici ta yi, ta ce, "You don't know anything Hammad. Ka manta cewa Kawu Imrana shi ne mahaifin Yaya Deedah?" "Ban manta ba Yaya Maryama." "To kuma sai in kai ƙarar Abba wurinsa cewa zai haɗa ni aure da ɗan da ya haifa? Ka ga ai ba zai yiwu ba ko?" "Haka ne." Ya faɗa bayan ya zauna a gefenta. Yana tunanin abun yi. "To yanzu what's the solution Yaya?" "I don't really know Hammad, that's why am crying. Wallahi ba na son Yaya Deedah da aure, kamar son da nake maka shi ma irinsa nake masa. Ta ya zan iya yin zaman aure da shi?" Muhammad ya ce, "Ke ma dai Yaya Maryama, tun tuni na taɓa faɗa miki Malamin Islamiyyarmu ya ce yana sonki amma kika gwasale ni. Da yanzu an miki aurenki kin huta da wancan Yaya Deedah ɗin." Matsalar yaro kenan. Yanzu zai maka abun kirki, yanzu kuma zai ɓata maka rai. Da hannu ta dakatar da shi, haɗe da faɗin, "I need to rest Hammad. Je ka ɗakinka." Babu musu kuwa ya miƙe jiki babu ƙwari, har ya kai bakin ƙofa ya juyo, ya ce, "You've to stop crying Yaya, move on. Ƙila ma shi Yaya Deedah yana can yana jin daɗinsa, ke kuma kina nan kina ta famar kuka. Idan fa wani ciwo ya kama ki? Na tafi, good night." Ya ja mata ƙofar bayan ya fita. Zaune ta tashi Maryama, ta cire hijabinta ta ajje a bisa gadon, kwantaccen gashinta da Mama ta tsefe mata kalaba ya bazu a bisa bayanta, ya sha mai sosai. Ta haɗa tafukan hannayenta a bisa kyakkyawar fuskarta, ruwan hawaye na zuba a samansu.  Mafita take nema daga wurin Allah, Ya yaye mata dukkan damuwarta. Tsantsar ƙiyayyar Deedah na daɗa shiga cikin zuciyarta. "Ya Allah!" Ta faɗa haɗe da komawa bisa gadon ta faɗa tim! Tana mai rasa dukkanin nutsuwarta. * Tun ɗazu yake zaman jiran zuwanta, amma shiru ba ta zo ba. Sosai ya shiga cikin damuwa, har ya fara ƙoƙarin zubar da ƙwallansa. Me ya hana ta zuwa ta ba shi magani? Ya tambayi kanshi. Gyaɗa kan nasa yake, yana mai jin tsananin kewarta na shiga duk cikin wata gaɓa ta jikinshi. "Ta ce ba za ta taɓa tafiya ta bar ni ba. Wai za ta zame min tamkar Amrata, za ta zama madadin Amrah a duk sadda na buƙaci kasancewa kusa da ita." Tamkar mai hankali haka ya yi wannan maganar. Ya daure miƙewa bisa ƙafafuwansa, yana mai tsananin jin yunwa. Kodayake ba mai hankali ba, amma fa ya tabbatar ba lafiya ba. Ba a taɓa fashin kawo masa abinci ba. Amma ga shi yau tun na rana ba a kuma kawo mishi wani ba. Kuma wacce ke kawo mishin ma babu ita. Bakin drowar da magungunansa suke ya nufa, kamar yadda ya ga Maryama na masa shi ma haka ya yi. Ya ɓalli magungunan iya wanda take ba shi, sannan ya buɗe deep freezer ya ɗauko robar ruwan Sona, ya kafa a bakinshi haɗe da maganin ya shanye. Bayan ya gama ya koma bisa gadon nashi, ya kwanta a takure, yana jin yadda damuwa ta turnuƙe zuciyarsa. Ya saba da ita. Ya saba da kyautatawarta, amma ga shi yau babu ita, ita ma ta masa nisa kamar yadda Amrah ta masa. Ko ranar da za su yi walima sai da ta sanar da shi cewa ba za ta dawo da wuri ba. Kuma tana dawowa sai da ta zo inda yake. Amma yau ba ta zo ba, ba ta shigo inda yake ba tun sadda ta kawo masa abincin rana. Tashi ya yi zaune kuma, ya ƙurawa ƙofa ido, a tunaninshi ko zai ga ta shigo. Amma ina, ko motsin mutum babu, alamun dai ba za ta zo ɗin ba kenan. Takaici ya dame shi, ya kama wuyar rigarshi da ƙarfin gaske, ya ɓarka ta, har sai da ta dire ƙasa. Laɓɓansa yake tauna da iya ƙarfinsa, take jini ya fara fita daga cikinsu, duk suka farfashe. Da wannan damuwar barci ya ɗauke shi zaune, sai dai kawai ya ɓingire bayan barcin nasa ya yi nisa. *** Kwanan Sans goma a asibiti aka ba shi sallama. Sai dai kuma, ba ya iya tafiya da ƙafafuwanshi, sanadiyyar bullets ɗin da suka shige shi ba su fice ba, ciki suka zauna, har sai da suka illata shi. Da ƙyar ma likitocin suka samu nasarar fitar da su. Tsananin tashin hankali Sans ya shige shi. Yau wai shi ne ya zama gurgu, ko kaɗan ba zai iya tafiya da ƙafarsa ba. Wa'yannan bayin Allah'n da suka taaimaka masa, su suka haɗa kuɗi suka siyo masa keken giragu, wanda ba ma sabo ba ne, tunda su ɗin kansu rufin asiri ne gare su. "Tunda an sallame ka, ina za ka nufa yanzu? Ko za ka amince ka zauna a gidanmu?" Babban yayan wancan ɗin ya faɗa, yana mai kallon Sans da dukkan hankalinshi. Runtse idanuwansa ya yi Sans. Ko kaɗan ba ya marmarin ci gaba da zama a Borno State. Jiharsu, inda kaf ƴan uwa da danginsa suke. Ba don komai ba sai abin da ya faru, kowansa da ya rasa, saboda wannan tashin hankalin da ake ciki. "Ba zan iya ba. Ba zan taɓa iya ci gaba da zama a garin nan ba." "To sai ina? Ko kana da dangi a wani garin ne?" "Ku kai ni ko ma ina ne. Amma dai in fita daga cikin jihar Borno." "Kar ka yi haka Salman. Ya kamata ka ɗauki ƙaddararka, ka sani cewa kowanne ɗan-Adam yana da tashi ƙaddarar. Allah bai manta da kai ba, zai kawo maka ɗauki a kodayaushe ne" "Ku kai ni tashar mota don Allah." Babu musu suka taimaka mishi suka saka shi a mota, kai tsaye suka nufi babbar tashar garin da shi. "Wane gari za ka je to?" "Katsina." Ita ta faɗo masa a rai, ita kuma ya faɗa. Ba wai don ya san wani a can ba. Kurum zuciyarsa ta ƙisima masa can ɗin, ya kuma aminta da hakan.. *** *A yi maneji da wannan.* *Masu mutunci kar a manta da kankaro mutunci.* Thanks all. Pinky durling💞 RAZ 2 [9/4, 4:31 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 5⃣5⃣ Wattpad: PrincessAmrah *** Kallonta ya yi cikin idanuwa, yana nazartar yanayin nata. Cikin sanyin murya ya furta, "Ki yi haƙuri Fiddou, ko kaɗan ban yi hakan da nuhin ɓata ranki ba. Soyayya ce ta ja, ita ce sila Fiddou. Don Allah ki duba lamarin nan, ki min kwatankwacin koda rabin ƙaunar da nake miki ce." Shessheƙar kuka take, tana mai ƙoƙarta ɗauko rinannun idanuwanta ta kalle shi. Dusasshigar muryarta da kuka ya gama disasharwa ta buɗe, ta ce, "Na amince zan aure ka Mahmouda. Na yarda, na kuma tabbatar cewa kai masoyina ne na gaske. Amma ina so ka san wani abu, cewa soyayyar Modu na nan ta yi zaman daram a cikin zuciyata. Ba zan taɓa iya hidda ƙauna tai daga raina ba. Ya riga ya bi jini da jikina. Idan ka amince za ka iya a hakan to, idan kuma ba za ka iya ba ka tahi, zan iya ci gaba da rayuwata a haka ba tare da na auri kowa ba." Cike da mamaki ya ɗago fuskarsa ya kalli Fiddou. Shin da gaske ne kalaman da yake ji daga bakinta? Da gaske ta amince za ta aure shi? Kamar a mafarki yake jin lamarin. Abin da bai tsammani ji ba kenan, saboda tun sadda ya zo wurinta take ta faman kuka, ta gagara furta komai. "Na gode ƙwarai da damar da kika ba ni ta aurenki Fiddou. Na miki alƙawarin zan kyautata miki, zan kula da ke, zan ba ki dukkanin gata da ya kamata ɗiya mace ta samu." Ba ta furta komai ba, sai dai kuma har yanzu ba ta daina kukan ba. Kanta sunkuye a ƙasa tana wasa da ƴan yatsunta. "In dai har kin shirya, to ina ga ba ma za a ɓata lokaci ba a yi auren ba. So nake na cika burin da mahaifiyata ta tafi da shi a ranta, ba tare da ta ga tabbatuwarsa ba. Abin da nake so da ke yanzu, don Allah de ki daina kukan nan, kar a je wata cutar ta kama ki. Bari in tashi in wuce, gobe da yamma zan dawo, ki faɗa wa Yaya Labib ɗin." Miƙewa ta yi bayan shi ɗin ma ya miƙe. Ta masa sallama sannan ya fita daga gidan, tana mai bin sa da kallo har ya fice. Ba wai son shi take ba, har ga Allah ba ta da wanda take so sama da Modu. Amma ya za ta yi? Ba ta da zaɓin da ya wuce ta amince da soyayyar Mahmouda, saboda aikin banza take, Dakon Son mahaukaci, da yanzu haka ya gama mantawa da ita ma. *** Su suka biya mishi kuɗin motar da kansu, sai da suka tabbatar motar ta tashi, sannan suka bar tashar, cike da tausayinsa. Tafiya daga Maiduguri zuwa Katsina ba wasa ba ce. Sosai suka sha zaman mota, wanda har sai da suka yi branching a Abuja suka kwana, saboda ta can suka bi. Dukkanin hanyoyin da za su bi a sauƙaƙen babu kwanciyar hankali, dole sai mai tsayi. Washe gari da asubar fari suka kama hanyar Katsina, ta Dikko ɗakin kara, daga babban birnin Abuja. Kamar yadda yake tun barowarsu Maiduguri yanzu ma haka yake. Ya haɗa kansa da guiwa, tunanin duniya kawai yake. Rayuwarsu ta yarinta yake tunowa. Soyayya da gatan da iyayensa suka gwada masa, da kuma ƙaunatayyar da ke tsakaninshi da ƙanwarsa Yamaira. Wa ya sani a Katsina? Shin idan ya sauka ina zai dosa? Ya makomar rayuwarsa za ta kaya a garin da bai taɓa zuwansa ba? Duka wannan jerin tambayoyi ne da yake ta yi ma kansa su, sai dai kuma bai da amsoshinsu, wannan dalilin ne ya sa shi haɗa kai da guiwa, tun jiya da suka baro Maiduguri. A Kaduna suka tsaya, da nufin duk wani mai uzuri ya yi, mai cin abinci ya siya, saboda a wani babban gidan mai ne suka tsaya. Zaune yake bai fita ba, sai kallon jefi jefin mutanen da ke shige da fice a farfajiyar gidan man kawai yake. Ji ya yi an dafa shi, da sauri ya karkato da dukkanin hankalinsa zuwa ga mutumin da ya taɓa shi ɗin, yana son sanin dalilin haka. "Yaro na kula da kai, tun jiya da muka taho a yadda kake haka kake. Shin me ya yi zafi shi ba wuta ba? Ko ruwa sau ɗaya tal na ga ka sha, bare kuma ai maganar abinci. Ban san damuwarka ba, kuma ba na so na sani. Amma ka fauwalawa Allah dukkanin lamurranka. Ka nemi abinci ka saka ma cikinka, maganin shiga wata damuwar ko kuma ciwo." Ya ji daɗin kalaman mutumin sosai. Hakan ya sa shi ƙirƙiro murmushi, haɗe da furta, "Na gode." "Ba sai ka min godiya ba. Ka faɗa min abin da kake son ci. Ga lemu can, ga nama, ga doya da ƙwai, me kake so?" "Lemun dai ya wadatar." Sans ya faɗa yana kallon mutumin. "Bai kamata ka sha zallar lemo ba, duk yunwar da ka kwaso tun jiya. Bari dai in siyo maka doyar, sai in haɗo maka da lemun." "To shi kenan, na gode ƙwarai." Ya karkace aljihunsa, da nufin fiddo kuɗin abincin ya ba mutumin, cikin wanda bayin Allahn nan da suka taimake shi suka ba shi. "Ba sai ka ba ni kuɗinka ba. Bari in siyo maka." Godiya ya sake yi wa mutumin, yana kallonshi ya sauka daga luxirious ɗin, ya nufi wurin mai doya da ƙwai. Mintinsu kusan arba'in a wurin suka tafi, ba kuma su tsaya ba har sai da suka je Malumfashi, aka tsaya saboda masu uzuri. Roƙar wancan bawan Allahn ya yi Sans, cewa ya taimaka masa zai yi fitsari. Tallabar keken nasa ya yi ya fitar, ya buɗe shi sannan ya kama Sans ya fitar, ya zaunar da shi a bisa keken, haɗe da tura shi. Da taimakonsa ya yi fitsarin, sannan suka dawo, suka ci gaba da shan hanyar Katsina. Shigarsu ƙofar Katsina ne hankalin Sans ya ƙara tashi, tuna cewa bai da wurin zuwa fa. A wannan lokacin kam hawaye ne ya kufce masa, mai cike da zallar damuwa da tashin hankali. Yana jin yadda wasu ke faɗin a sauke su nan a sauke su can, shi dai ya yi shiru, har sadda aka isa tasha da shi. A lokacin har wancan mutumin mai taimakonsa ya sauka, wanda inda a ce Sans ya faɗa masa ba shi da wurin zuwa, mai yiuwa ne ya taimaka mishi. Cikin hikima ya samu ya fito daga motar, bayan kowa ya watse, sai shi kaɗai. Kimanin ƙarfe uku da rabi na rana kenan, daf da la'asar. Tashar a cike take kamar koyaushe, kowa na harkar gabansa. Ajiyar zuciya kawai Sans ke saukewa, yana tunanin mafita. Lalubar aljihunsa ya yi, ya zaro kuɗaɗen da suka masa saura, kimanin dubu takwas da ɗari biyar. Gama ƙirgar kuɗin kenan yana ƙoƙarin miyarwa aljihu, fit! Ya ji an warce su, ya ɗaga kanshi ya ga mutum sai tiƙar gudu yake. Ihu ya kurma haɗe da faɗin, "Ku riƙe shi, kuɗina ya fige min." Amma ina, tuni ya yi nisa, har ma ya fita daga cikin tashar. Mutane ƴan tasha sai masifa suke ma Sans, wai don me ya san halin tasha zai yarda ya fiddo kuɗi, yana ƙirgawa a gaban mutane? Kansa kawai ya dafe, yana jin zuciyarsa na masa zafi, tamkar za ta tsage ta fito waje. Wannan wace irin rayuwa ce? Wane irin zamani ne muke ciki, wanda ake miyar da abububuwan banza ba a bakin komai ba? A ce wai mutum yana ji, yana gani a fige masa kuɗi daga hannu? Ji ya yi baki ɗaya tashar ta fita ransa. Mutanen da ke cikinta ɗai-ɗaiku ne na kirki. Daga masu shaye-shaye sai masu faɗace-faɗace, ana zage-zagen banza. Gurgura kekensa ya yi, ya bar harabar tashar ma baki ɗaya. Babu nisa daga nan zuwa wani masallaci. A bakin masallacin ya tsaya, cikin hikima ya gabatar da alwalla, sannan ya ajje keken bakin ƙofar masallacin, da rarrafe ya shiga ciki, ya gabatar da duk sallolin da suke kanshi. Bayan ya gama ya ɗan kishingiɗa, da niyyar hutawa, nan barci mai nauyi ya ɗauke shi, saboda already an yi sallar la'asar an gama a masallacin. Bai ankara ba ya ji wani mutumi na bubbuga shi, cewa ya tashi za a yi kiran sallar magrib. Cikin mamaki ya tashi zaune, yana murtsika idanuwanshi, yana mai leƙen ƙofa, idanuwansa suka yi tozali da duhun da garin ya fara. Bayan sallar ishai ya fara ƙoƙarin gyara kwanciya, ya ji wani mutumi na bubbuga shi, cewa ya tashi, an hana kwana a masallaci yanzu, rufe shi ake saboda ɓarayi. Kamar ya kurma ihu haka ya ji. To shi yanzu ya zai yi? Ina zai tafi ya kwana? Bai da yadda zai yi haka ya miƙe, ya rarrafa har zuwa bakin ƙofa, ya jawo kekenshi ya hau, yana mai tura shi a hankali, yana kuma tunanin mafita. Kuka yake sosai, damuwa na daɗa addabarsa, ba ya ko kallon gabanshi, har ya isa bakin titi. Ƙarar mota ya ji tiiii! Da ƙarfi ana neman kaɗe shi. Hakan ya kiɗimar da shi, ya rasa dukkanin nutsuwarshi. A masife matashin ya fito, hannunshi riƙe da karan sigari, yana faɗin, "Mallam ba ka da idanuwa ne kai? Yanzu da a ce ka ja na kaɗe ka fa? Azumi sittin kake so ya hau kaina?" "Yi haƙuri." Sans ya faɗa, yana mai sadda kanshi ƙasa. Rayuwarsa ta baya ta faɗo masa a rai. Irin dukiyar mahaifinsa, mota sai dai ya hau wacce ya ga dama. Amma wai yau shi ne a bisa keken guragu, har wani matashi da bai wuce sa'anshi ba yake kawo masa wargi, kuma ya biye shi da ban-haƙuri. Zuciyar matashin mai taushi ce. Haka kawai haƙurin da Sans ya ba shi ya sa shi jin tausayinshi. Fuskarsa ya kalla da hasken mota ya dalle shi. Kyakkyawan saurayi ne, fari sol da shi, mai cikar zati. Sai dai fuskar tasa da raunukan da ba su gama warkewa ba, amma duk da haka ba su hana kyawunsa bayyana ba. Duƙawa ya yi a gaban Sans, cikin kulawa ya ce, "Me yake damunka bawan Allah? Da alama kana cikin matsananciyar damuwa." Hawayen fuskarshi ya share Sans. Ya ce, "Babu komai bawan Allah. Je ka kawai." Miƙewa ya yi matashin, ya juya zai nufi motarsa. Har ya isa bakin motar kuma ya fasa, ya juyo cikin takunshi, ya iso gaban Sans, yana faɗin, "Ba zan tafi in barka a haka ba, a cikin daren nan. Idan ni an ci sa'a ban kaɗe ka ba, ban san wanda za ka haɗu da su a gaba ba." Shiru kawai Sans ya yi, ba tare da ya furta komai ba. "Ka amince ka bi ni mu tafi." Matashin saurayin ya faɗa, yana kallon Sans. Kai kawai ya ɗaga mishi, hakan ya ba shi damar tura keken na Sans, ya isar da shi gaban motar tashi, ya saka shi a ciki, sannan ya ninke keken ya saka a bayan motarshi. *** Washe gari tunda asuba ta fara tariyar abubuwan da suka faru jiya. Da gaske ba ta koma wurin Modu ba tun bayan da Mama ta fara mata maganar Deedah. Kenan hakan na nufin ta saɓa alƙawari, ba ta ba shi maganin dare ba? Gyaɗa kanta take, tana mai tsananin jin haushin kanta. Haushin da take ji a yanzu, ji take ya ninka na aura mata Deedah ma da ake son yi. Kuka ta fasa mai ƙarfi, tana ambatar, "Na saɓa alƙawari. Allah ka gafarta min ya Allah. Yanzu me zan faɗa ma Yaa Noor? A wanne hali ya shiga bayan babu ni? Allah Allah!" Ta dafe kanta, a saman sallayar da take zaune. Wayarta ta zaro daga jikin caji, ta duba ta, a silent take tun jiya da ta saka, hakan ya sa ba ta ga duk kiran da ake mata ba. Abun mamaki, har da Dr. Hamdan M. Ramat ya kira ta, da kuma sunan Bobby, wanda ya mata kira kusan guda goma sha biyar, shi ne ma ƙarshen ɗaga wayarsa da ya yi, kafin ya galabaita. Mamaki take, ta yadda likitan da kanshi ya kira ta, duk kuwa da ayyukan da suke gabanshi. Kuma ba haka suka yi ba, sun yi ne cewa ita za ta kira shi ƙarfe takwas, amma abun mamaki, shi da kanshi ya kira ta. Kawar da mamakinta ta yi ta hanyar miƙewa tsaye, ta ninke sallayar ta ɗora a bakin gado, sannan ta doshi barin ɗakin, zuwa na Modu. A takure ta same shi, ya haɗa kai da guiwa, yana ta wani irin kuka mara sauti, sai dai shessheƙarsa kawai ake ji. Cikin kiɗima ta iso gare shi. Hannunta a ka take faɗin, "Ya Noor me ya faru da kai?" Tunani yake, mafarki ne wannan yake yi. Irin zuwan da Amrah ta saba yi masa a mafarki ne ita ma Maryama ta masa. Hakan ya sa ya ƙi ɗago kanshi, yana mai tsananta kukan da yake yi. "Ya Noor me kake ne wai haka? Ko wani abu yana maka ciwo ne?" A nan ɗin ma bai ɗago kanshi ba. Haka kuma bai rage sautin kukan ba, sai ma ƙarfafa shi da ya yi. Hankalinta ne ya daɗa tashi. Ta sa hannunta tana mai dafa kafaɗarshi, a hankali take ɗan bubbugawa. "Zan yi fushi ma in tafiyata, tu da dai ba za ka min magana ba." Taba shin da ta yi ne ya ba shi tabbacin ba mafarki yake ba. Ya dago kansa, da idanuwansa da suka gama rinewa. A kidime ta zaro idanuwanta tana kallon bakinshi. Ta ce, "Yaa Boor me ya samu bakinka? Na shiga uku? Ko wani abu ya faru ne?" Daina kukan nashi ya yi, ya dora dukkanin idanuwansa gare ta, yana bin ta da wani irin kallo, mai cike da zallar jewarta da ya yi. "Yaa Noor talk to me. Me ya faru da labbanka duk suka farfashe?" "Yo ni na ciccije su." Ya fada cikin halin ko'inkula. Farin cikinshi dai da ta dawo garr shi. Ita kam ba ta masa nisa kamar yadda Amrah ta masa ba. "Me ya sa za ka ciccije labbanka?" Ta tambaue shi, cike da al'ajabi. "Ba ke ce kika ki zuwa ba? Ni kuma na ji haushi, na keta riga ta, na kuma ciccike labbana." Ya fashe da dariya, yana mai sadda kanshi, wai ya ji kunya. Samun kanta ta yu da murmusawa. Har cikin ranta ta tausayawa masa. Wani irin dadi ta ji ya ziyarci zuciyarta. Ashe har Annur ya damu da ita haka? Kodai ya fara ba ta matsayi ne kamar Amrah? Ba ta samo wannan amsar ba ta juyo muryarsa yana fadin, "Ke kika ce ba za ki taba yi min nisa ba, za ki zame min madadin Amrah." Habarta ta dafe da hannun dama, tana tuna ranar da suka yi wannan maganar da shi, tamkar hankalinshi ba ya gare ta. Amma ga shi har bai manta ba, har ma ya fara yarda cewa babu Amrah. Lallai ta yarda sosai da Dr. Sandra. Ta amince cewa Lost of Memory shi ne bbsvbar damuwar Annur. Bayanan da ta mata cewa makusanci yake nema, wanda zai nuna masa dukkanin soyayya, ya ba shi dukkanin kulawar da wani masoyi zai samu daga wurin masoyiyarsa. Yau ga tabbaci ta gani. Har Annur na ambatar za ta zame masa madadin Amrah. "Ko jiya ma ta zo min a cikin barci, ta ce da ni wai in dauka cewa ke ce ita, in moyar da duk wata soyayyarta gare ki, wai in dai ina so ta yi farin ciki. Farin cikin Amrah nake so! Duk abin da zai faranta mata rai ina biye da shi, hakan ya sa na mata alkawari cewa zan miki kauna, sai dai ba kamar wacce nake mata ba. Ta yarda da hakan, kuma ta bace da ganina, hade da raubtsuwar ba za ta taba dawowa a gare ni ba har abada." Kuka ya fasa a daidai nan, yana mai kallon wuri daya, tamkar wanda yake tunkwa da wani abu. Tun sadda ya fara maganar take kallon shi, kallon mamaki. Wai kodai Annur ya warke daga hauka ne? Wannan kalaman da yake mata, mahaukaci ba zai taba iya yin su ba. A hankali take jin duk wata damuwarta tana rarewa izuwa farin ciki. Kaunar Annur na shiga duk wata kusurwa da ke cikin jikinta. Soyayyarsa na ambaliya a jini da dukkanin jijiyoyinta. Ji take ta manta ma da wata damuwa da take cikinta. Maganar auren da ake so a hada ta da Deedah nna disashewa daga cikin zuciyarta. Tana canzuwa da farin cikin da Annur ya jefa ta a ciki. "Kawai a zo a mana aure..." Ta tsinkayo muryarsa ya fada, yana mai sadda kanshi kasa, alamun jin kunya. *** *My pipu how was this chapter? Was it nice? In ga hannuwan wanda ta ma dadi...lol.* *To kar dai a manta da kankaro mutunci.* *Masu mutunci ku karkata ku kankaro shi.* *Ni ma sai in karkata in kankaro muku dogon shafi irin na yau.🤗😘😃* *Ku kuma ghosts masu hancin yalo, ku ci gaba da labe, Allah yana ganinku. Kuma insha Allahu gobe sai kun tashi karanta next oage dina chajin wayoyinku ya kare. Ehen. Masu hakoran bera kawai.😏🤒* *Jinjina ga yan RAZ NOVELLA 1&2. Ina kaunarku all fisabilillah. Iya wuya ana tare.* Thanks all. Pinky durling💞 RAZ 2 [9/6, 11:23 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 5⃣6⃣ Wattpad: PrincessAmrah *** A bakin wani gidan gona suka faka motarsu. Tun sadda suke shigowa cikin dajin Sans ke son yin magana. Yana son sanin ina za su je da suke keta daji irin haka. Sai dai ya yi shiru ne saboda ya san wasu ba su son yawa magana. Zai haƙuri har su isa ɗin, don ya ga iya gudun ruwansu. Taimaka masa ya yi matashin ya fiddo keken daga bayan motarsa, ya ajje a daidai ƙofar gaba da ya buɗe ma Sans, sannan ya tallabo shi ya ɗora a bisa keken. Bayan ya zauna daram ya rufe murfin motar, sannan ya ringa tura shi har suka isa daga bakin ƙofar, ya hau ƙwanƙwasawa. Babu jimawa sai ga wasu matasa sun fito, ɗaya na magagin barci, ɗayan kuma yana ma wancan saurayin sannu da zuwa. "Yax. A kama shi a shigar ciki, zan gyara parking ɗina." "To Oga." Wanda aka kira da suna Yax ya faɗa, yana mai kama keken Sans, haɗe da shigar da shi cikin gidan. Bayan sun ƙarisa tangamemen falon, Yax ya ce da ɗayan abokinsa, "Esien, taimaka kawo mishi ruwa ya sha. Da alama yana jin ƙishi, ga bakinsa nan duk a bushe." Bai musa ba Esien, ya nufi inda fridge yake, ya ɗauko masa ruwan roba, mai tsananin sanyi, har da raɓa. Miƙa ma Sans ɗin ya yi bayan ya buɗe, bai karɓa ba, sai cewa ya yi, "Ina jin zazzaɓi sosai a jikina, ba zan iya shan ruwa mai sanyi ba. Kuma ga magungunana nan a cikin aljihu ina son sha, ba a sha da ruwan sanyi." Wancan matashin da daidai shigowarsa kenan ya ce, "Esien kawo masa mara sanyi don Allah. Wanda ba a saka a fridge ba." Ya ƙariso gaban Sans, da faɗin, "Sannu ko?" Kai kawai Sans ya jinjina masa. Esien na kawo masa ruwan ya ɓalli magungunanshi ya sha. Sanann ya ce, "A ina zan yi wanka? Ku taimaka min, duk jikina babu daɗi." "Yax, ka dafa masa ruwan zafi yanzu. Da alama akwai zazzaɓi sosai a jikinsa, bai kamata ya yi wanka da ruwan sanyi ba." Cikin bin umurnin wancan matashin ya miƙe, ya ƙarisa cikin kitchen domin ɗora ruwan zafin. "Ka kwantar da hankalinka. Ni sunana Farouk Sardauna, you can call me Bobby. Za ka iya ci gaba da zama a nan tare da wa'yannan bayin Allahn, duk yarana ne, har sadda ka samu wurin zuwa." Kansa kawai ya jinjina ma Bobby. Yana mai samun dukkanin nutsuwarsa da ya rasa a baya. Sai da Yax ya haɗa mishi komai sannan ya sanar da shi ya haɗa masa, ya tura shi har toilet ɗin, sannan ya bar shi ya yi. Bayan Yax ya dawo, Bobby ya ce da su, "Ina son ku nutsu mu yi magana da ku." "To Oga." Suka haɗa baki wurin faɗi. "Wannan da kuke gani, ina son duk wani girma da za ku ba ni, shi ma ku ba shi. Ku girmama shi, ku ɗaga darajarshi, matuƙar kuna son ganin farin cikina. Duk wani abu da yake da buƙata, ku tallafa masa, tunda kun gan shi gurgu." Cikin gamsuwa Esien ya ce, "Mun maka wannan alƙawarin Oga." Yax ma ya ce, "Deal!" Tafa hannunsa ya yi Bobby, ya ce, "Shi ya sa nake alfahari da ku a kodayaushe. Kuna faranta min rai sosai. Duk abin da zan nunar muku da ina so kuna aikata shi." Yax ya ce, "Ai Oga dole ne mu faranta maka, saboda kai ma kana faranta mana. Ka duba ka ga, ba wani aiki sosai muke yi a gidan gonar nan ba, amma duk sadda Dadynka zai zo ka ringa koɗa mu kenan, yana mana kyautukan ban mamami. Tsakaninmu da kai sai dai godiya kawai." Murmushin jin daɗi ya yi, sannan ya shiga ɗakin da kayanshi suke, wanda idan ya zo gidan yake sakawa. Wasu kayan sanyi ya fiddo ya ɗora a bisa gado, ya feshe su da turare, sannan ya dawo falon. Ya tarar har ya fito daga wankan Sans, hakan ya sa ya tura shi izuwa ɗakin da ya fito daga shi ɗin. Mai ya gwada mishi ya shafa, sannan ya ba shi kayan, yana mai fita daga ɗakin. Abincin da ya tsaya ya siyo ne ya koma ya ɗauko daga cikin mota, ya mimmiƙa ma su Yax nasu sannan ya ajje ma Sans nashi gefen kujera, shi ma ya hau cin nashi. Ƙarar keken Sans da suka ji ne ya tabbatar musu cewa ya fito, duk suka ɗaga kawunansu suka kalle shi. Sosai kayan jikinshi suka amshe shi, tamkar dama can nashi ɗin ne. Bayan ya iso gaban Bobby ya fasa kuka, yana mai runtse idanuwansa. Da sauri Bobby ya ajje robar take away ɗin, yana tambayar Sans dalilin yin kukan nashi. "Kawai ina jin daɗin halaccin da ka min ne. Har ma ban san ta hanyar da zan bi don na gode maka ba." Gyaɗa kansa ya yi Bobby, cike da tausayi ya ce, "Ka daina kuka in don wannan ne. Har ga Allah ka shiga raina, a lokaci guda na ji tausayinka ya shiga duk wata gaɓa da ke cikin jikina. Karɓi wannan." Ya miƙa masa wani hankici babba, mai ɗauke da tambarin tutar USA. "Share hawayenka, kar kuma na kuma ganin koda ɗison hawaye ne ya fito daga idanuwanka." Karɓar kuwa ya yi Sans, yana mai share hawayensa, da hankicin.  "Yauwa ko kai fa. Yanzu sai ka ci abincinka. Daga nan sai ka samu ka kwanta, ko za ka samu ƙarfi-ƙarfi a jikinka. Gobe da safe zan dawo insha Allahu, zan kai ka asibiti." Godiya Sans ya sake jaddada masa, sannan ya fara cin abincin, zuciyarsa na cike da ƙaunar bawan Allahn da ya ba shi taimako ba tare da ya san cikakken asalinsa ba. *** Bubbuga shi ya ji an yi, a lokacin da kanshi yake bisa guiwowinsa, yana saƙe-saƙe haɗe da zancen zuci. Ɗago kan nashi ya yi, yana kallon mai taɓa shi ɗin. Dadynshi ya gani sanye da farin glasses, yana sakar masa murmushi. "Ya ƙarin haƙuri?" Dadyn nashi ya faɗa, yana mai ƙoƙarin gyara zamansa a kusa da Sans. Share guntuwar ƙwallarsa ya yi, ya ce, "Haƙuri an gode Allah, Dady." Yana mai jin nauyin Dadyn nashi, wanda shi kanshi ya kasa gane dalilin hakan. "Allah Ya ji ƙan Farouk, Ya sa ya huta. Ka yita haƙuri ka ji? Na sani, akwai zafi da raɗaɗi. Akwai ciwo mai tsanani, mutuwar babban aboki. Amma ka daure, ka kai zuciyarka nesa. Ba wai gaggawar tafiya ya yi ba, lokacinsa ne ya yi." Dady ya ɗan yi shiru daga nan, yana karantar yanayin ɗan nashi, wanda hakan ya ƙara sagar masa da jiki. Cikin kwantar da hankali ya ci gaba da faɗin, "Dukkan mai rai mamaci ne, Annur. Yanzu ina Amrah take? Ka manta irin soyayyar da kuka yi da ita? Ka ga kuma, a hakan Allah ya ɗauki rayuwarta. A haka ka ci gaba da rayuwa kamar kowa. Ka jure, ka yi haƙuri, duk da dai kalar ƙalubalen da ka fuskanta a lokacin da ta rasu. Ba na so a kuma ƴar gidan jiya Annur. So nake ka miyar da komai ba komai ba. Ka ci gaba da yi ma Farouk addua, har sadda kai ma taka mutuwar za ta zo ta ɗauke ka." Tun daga sadda Dady ya fara yi mishi maganar Amrah yake jin gabanshi na faɗuwa. Shi da bai santa ba, bai taɓa ganinta ba, amma ya ci gaba da rayuwa a idanuwan duniya a matsayin shi ne asalin masoyinta. Sau da dama shi kanshi yakan zauna ya yi tunani; makomar rayuwarsa a duk sadda wancan ƙullin ya kwance. Ga shi abokin shawarar nashi babu shi a yanzu, ya kwanta damarsa. Kodai zai fito ya fallasa kanshi ne? Ya tambayi kanshi. Da sauri wata zuciyar ta inigiza shi haɗi da kwaɓar kanta, cewa kar ya yi. Ta ya zai ci gaba da rayuwa a duk sadda asirinsa ya tonu? A ina zai ci gaba da zama? Dama Allah ne gatanshi Bobby ne gatanshi, tun ma kafin ya dawo gidan su Annur ɗin. To babu Farouk yanzu, ya zai yi? Zai rufe bakinshi salin-alin ya ci gaba da rayuwa a gidan. Sai dai ya tsara ma kanshi, cewa babu shi babu kayan maye har abada. A duk sadda zai ga mai yi ma zai Ƙoƙarta kwaɓarsa, saboda shi ya ga illarsa, a zahiri ba nesa da shi ba. *** Cike da ƙarfin hali take taya Mama aikin haɗa kalaci. Raba-da-rabi take jin daɗi a zuciyarta. Nan daɗi, can kuma haushi; Auren dole da ake son a mata. Daɗin kuwa na kalaman da suka fito daga bakin Annur ne, masu cike da zallar nishaɗantar da zuciyarta, da duk gaɓɓan jikinta. Bayan sun gama duka ta kai a ɗakin Abba, ta samu har ya gama shirin fita Office, kalacin kawai yake jira. Gaishe shi ta yi cikin girmamawa, banza ya mata, ko kallon inda take bai yi ba. A zatonta ko bai ji ba ne, hakan ya sa ta sake ɗaga sautinta, ta gaishe shi. Bai mata magana ba, sai ma Hammad da ke daidai shigowa ɗakin da ya ma magana, cewa ya je ya kira Mama. Jiki babu ƙwari ta fice daga ɗakin, wasu irin zafafan hawaye na fita daga idonta. Tun daga jiya take kuka, babu ci babu sha, sai famar ciwon kai, wanda panadol ya kasa saukarwa. A bisa faffaɗan gadonta ta faɗa. Haushin kanta take ji sosai, ta yadda zuciyarta ta kasa aminta da zaɓin iyayenta. Ba ta ga laifin Abba ba, ko kaɗan. Da gaske ko ita ce ba za ta taɓa aikata abin da take so Abban nata ya yi ba. Bai kamata ba, a yadda kawu Imrana ya yi hidima da Abbanta, kuma ya iya ya tinkare shi da zancen wai ba ta amince da auren Deedah ba. Muhammad da shi kanshi bai ji daɗin abin da ya faru ba, bayan ya kira Mama zuwa ɗakin Abba, ya lallaɓa ya shiga ɗakin Mamar da shirinsa na makaranta, ya ɗauko wayarta, ya ɓoye a cikin rigarsa. Da sanɗo da sanɗo yake tafiya, har ya fita daga part ɗin nasu, ya nufi wani part da ke can baya, inda babu kowa. Lambar Kawu Imrana da aka rubuta ma Yaya Imran ya gano, babu shakka bare tsoro, ko kuma tunanin wani abu, ya latso kiranshi. Har ta tsinke bai ɗauka ba, ya sake kiransa, tana daf da tsinkewa Kawu Imrana ya ɗauka. Sallama ya yi, haɗe da faɗin, "Hajiyar Maryam barka da safiya. Ya tashin iyali?" Sai a yanzu Muhammad ke jin faɗuwar gaba duk da kasantuwarsa ƙaramin yaro. A haka ya daure, ya ce, "Kawu ina kwana? Ni ne Muhammad." "To to to madallah da Muhammadu. Ya kuka tashi da iyayen naka?" "Suna lafiya." Ya faɗa a hankali. "Lafiya dai ko ɗana?" Kawu Imrana ya faɗa, cike da mamakin kiran da Muhammad ɗin ya masa da sassafen nan. Magana Hammad ya hau yi masa ƙasa-ƙasa, yana yi yana waigen gefe da gefensa, gudun kar a kama shi yana yi. Sai da ya yi kusan wayar minti bakwai, kafin suka yi sallama da kawun nashi, haɗe da lallaɓa komawa ɗaki. Ya ci sa'a kuwa har yanzu Mama tana tare da Abba, hakan ya sa ya lallaɓa ya miyar da wayar. Sai dai kuma ya manta shaf, domin kuwa yarinta ba ta bar shi ya tuna goge kiran ba. Fitowa ya yi fuskarsa a sake, haɗe da nufar ɗakin Maryama. A kwance ya same ta, tana ta faman kuka mai sauti. Ƙarisowa ya yi ya zauna a bakin gadon, cike da tausayin tilon ƴar uwarsa, mai ƙaunarsa, mai son farin cikinsa fiye da nata. Riyawa yake a ransa, duk yadda zai yi dole ya yi, don ganin ya kuɓutar da ita daga wannan mawuyacin halin da take ciki. Ya fara hawa hanya a yanzu kam, yiwuwar abun kawai yake jira. Bubbuga ta ya yi a hankali, yana faɗin, "Yaya Maryama..." "Leave me Muhammad!" Ta faɗa da ƴarfi, cike da takaici. Duk da ya ji haushin tsawar da ta masa, amma bai yi zuciya ba, ya sake faɗin, "Na miki alƙawari in dai ina raye to babu wanda zai miki auren dole. Wanda kike so shi za ki aura." Tashi ta yi zaune tana kallon shi. "Ta yaya?" Ta haɗa wannan kalaman biyu, da ƙyar da jibin goshi, duk da ba ta san ta yadda ta tsamo su daga cikin bakinta ba. "Just wait, you'll see." "Kar ka yi koma menene Hammad. Kar ka ja min, ina zaman zamana. Ka bari kawai, mu barwa Allah lamurranSa, Shi ne kawai zai iya magance mana." Kanshi ya gyaɗa mata, da murmushi ya ce, "Ba zan ja miki komai ba Yaya Maryama, I promise you." Kanta ta gyaɗa da hawaye kwance a bisa fuskarta, ta ce, "Allah ya tabbatar." Kafin ya sake faɗin komai ya ji muryar Mama na kiransa, cewa ya fito Abba ya wuce da shi makaranta. Tashi ya yi, ya mata ba-bye, sannan ya fice daga ɗakin, yana jin zuciyarsa wasai, tamkar babu wata damuwa a cikinta. *** A yi maneji da wannan, iya wanda ya samu kenan. Do comments Do votes and then share with your family and friends. Thanks all Pinky Durling RAZ 2 [9/7, 12:29 AM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taɓa zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 5⃣7⃣ Wattpad: PrincessAmrah *** Tun daga sadda Fiddou ta karɓi soyayyar Mahmouda yake duk iya ƙoƙarinsa na ganin ya koya mata son shi. Ya ɗan samu nasara kaɗan ba mai yawa ba. Domin kuwa a yanzu har murmushi takan yi duk sadda suke tare. Ko a gida ma yakan faɗo mata a rai har ta samu kanta da murmusawa. Sai dai kuma murmushin yakan gushe daga saman fuskarta, idan ta tuno da Modunta, wanda take ma mutuwar so. A tsawon wannan lokacin, har manya sun shiga maganarsu, an tsaida zancen auren nasu, wata ɗaya mai zuwa. A yanzu ne Aunty Sahiya ke nadamar abubuwan da ta kasance tana ma Fiddou. Ta tabbatar cewa cin amana ne fa take yi, kuma ba za ta so wata ƙanwarta ta faɗa tarkon matar yayanta ba, kamar yadda ta ringa cutar da Fiddou, ƙanwar mijinta uwa ɗaya uba ɗaya. Duk wata biyayya da ya kamata ƙarama ta ma babba, haka Fiddou ke ma Aunty Sahiya. Amma ita ta kasa karɓarta a matsayin ƙanwarta, ta kasa kyautata mata kamar yadda ita Fiddou ɗin take ƙoƙarin kyautata mata. Zaune take a ɗaki Fiddou ɗin. Ta rafka tagumi tana mai tunano tsawon lokutan da suka shuɗe, na zamantakewarta da rayuwarta da Modu. Shirmensa kawai take tunawa, da kuma sunan Amrah da ke yawan fitowa daga bakinsa. Sosai ta yi zurfi da wannan tunanin, hakan ya sa ruwan hawaye ya fara sauka a bisa kumcinta. Gyaran murya ta yi Aunty Sahiya, bayan ta ƙarisa shigowa ɗakin ta nemi wuri ta zauna, a kusa da Fiddou ɗin. Zabura ta yi Fiddou, ganin Aunty Sahiya ta shigo ɗakinta, kuma har ta nemi wuri ta zauna. Ta tabbata ba alkhairi ne a tattare da zuwan nata ba, sai tarin wulaƙanci da take tunanin zai fito daga bakinta. Da dukkan hannuwanta ta sa tana share hawayen, haɗe da furta, "Sanu da shigowa Aunty Sahiya." Abin da take tsammanin faruwarsa sam! Ba shi ne ya faru ba. Sai saɓanin haka da ta gani. Murmushi ne shimfiɗe a fuskarta, tana mai ƙara kallon Fiddou, cike da yanayin tausayi. "Yauwa Fiddou. Kukan ne halan har yanzu ya ƙi ƙarewa?" Mamaki bai bar Fiddou ta iya furta komai ba, sai kallon al'ajabi kawai da take bin ta da shi. "Ki yi haƙuri Fiddou, komai yai yi hwarko yana da iyaka. Kuma dukkan tsanani yana tare da sauƙi." Ba ta taɓa tsammanin Aunty Sahiya ta san hakan ba, haka kuma ba tai tsammanin akwai ranar da Aunty Sahiya za ta iya fuskantarta da irin wannan kalamin ba. "Fiddou magana nake son yi da ke, ta fahimta. Hwatar za ki mallaka mini dukkanin nutsuwa da hankalinki." Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke, ta ce, "Insha Allahu. Ke nake saurare." Matsowa ta yi daf da Fiddou, ta ce, "Gahwara zan nema a wurinki Fiddou. Na sani, na san ni ɗin ban zama ta gari a gare ki ba. Tunda na auri Yayanki Labib ban taɓa yin wani abu da nuhin hwarin cikinki ba, duk da kuwa naki ƙoƙarin na ganin kin ba ni girmana. Ki sani Fiddou, na yi da na sani, da na sani mara misaltuwa. Sai yanzu nake jin haushin kaina; rashin kyautata mikin da na yi, duk da kuwa ke ɗin kina da buƙatar mai kyautata miki. Don Allah Fiddou ki yafe min, wallahi na yi alƙawarin hakan ba za ta sake hwaruwa ba." Tana dakatawa a nan, da sauri Fiddou ta tsugunna a ƙasan Aunty Sahiya, tana kallon yadda take kuka, kuka mai tabbatar da ta nadama. Hannunta ta saka Fiddou, ta ringa share mata hawayen, tana faɗin, "Ki daina kuka Aunty Sahiya. Wallahi komai ya wuce. Allah Ya yahe muna baki ɗaya." Da haka suka rungumi juna, cike da ƙaunar junansu, tamkar babu wani abu da ya taɓa shiga a tsakaninsu. *** Sosai rayuwar Sans ta sauya, daga baƙin ciki zuwa farin ciki. Duk wani abu da zai nema yana samu, tamkar sadda yake gidansu. Kulawar da su Yax ke ba shi, ko shi ne Ogan nasu iya wanda za su ba shi kenan. Sosai suke girmama shi, duk da kasantuwarshi gurgu, ba ya neman komai ya rasa a rayuwarsa. A lokacin da Sans ya cika wata guda a gidan ne, Bobby ya fara ƙoƙarin karkatar da shi, ta hanyar koya masa shan cyrup, da niyyar duk wata damuwa da yake cikinta za ta gushe, izuwa wata duniyar ta daban. Daga farko sam! Sans bai yarda da hakan ba. Dalilin da ya sa ya butulce ma Bobby kenan, ya kuma ƙi karɓar wannan tayin nasa. Sai daga baya ne sadda damuwar tunowa da iyayenshi ta addabe shi, ya ringa tunanin tilon ƙanwarsa Yamaira, kwatsam Bobby na zaune da shisha a gabanshi, da kuma karan sigari a hannu yana zuƙa, sai tarin kwalaban cyrup a gabanshi, ya shanye wasu, bai fasa wasu ba. A zaune ya same shi ya yi mankas, amma bai fara fita daga hayyacinsa ba. Ƙoƙarta sauka daga keken nasa ya yi, saboda a tsawon wannan kwanakin har asibiti Bobby ke kai shi, inda yake da wani nurse abokinsa, yake ma Sans treatment. "In har da gaske kake cewa wannan abun zai gusar min da damuwar da nake ciki, shirye nake da ɗanɗanawa, a karon farko na rayuwata. So da dama nakan tuno da rayuwata ta baya, in tuno da kyautatawar da na samu daga wurin iyayena. To kuma lokaci guda na rasa su, sun tafi sun bar ni ni kaɗai a duniyata. Don haka dole in fantsama wata rayuwar ta daban, saɓanin wacce nake a kai sadda suke raye." Hannu ya ba Sans suka tafa Bobby, yana faɗin, "Ko kai fa abokina. Yanzu na ji magana. Ungo wannan. Ina mai tabbatar maka da zarar ka fara shan shi yau, to gobe kai za ka kawo kanka da kanka cewa in ƙara maka." Karɓar kwalbar ya yi Sans. A daidai zai kai kwalbar bakinsa, wani tunani ya faɗo masa a rai, cewa kar ya sha, ya yi ƙoƙarin kwaɓar zuciyarsa, da kuma ta abokinsa, a kan wannan mummunan halin. Wani sashe na zuciyarsa ne ya gargaɗe shi, kan cewa matuƙar fa bau aminta da wannan tayin ba, lallai zai dauwama a cikin damuwa, kamar yadda Bobby ya faɗa masa a baya. A bakinsa ya kai kwalbar, bai sauke ba har sai da ya shanye ta tas, har yana suɗar baki-bakinta. Ya ajje ƙasa, yana mai kallon yadda Bobby ke sakin murmushin jin daɗi. Tun daga wannan lokacin ne Sans ya ƙware a harkar, har ma ya nemi ya zarce Bobby. Suka ɓaci kuma da mugun son mata, da neman mata. Har a gida ake kawo musu matan. Yax da Esien ne suka koma tuƙin napep, duk don su ringa kawo ma su Sans mata suna musu fyaɗe. Idan sun yi fyaɗen kuma sai su sa su kai su can su yar, duk sadda suka farfaɗo su nemi hanyar tsira. Da wani yammaci ne, daidai irin ƙarfe shida na yamma, babban titin ring road babu kowa a kai, babu giccin ko babur bare mota.  Bobby na tukin mota sai Sans kujerar zaman banza. A tsayin wannan lokacin kam sosai Sans ya ji sauƙi. Baki ɗaya ya ma daina hawa kujera, saboda kyakkyawar kula da ya ringa samu daga wurin wannan nurse ɗin da ke asibitin Turai. Man motarsu ne ya ƙare, hakan ya sa Bobby yai yai ya tada motar amma ta ƙi tashi. "Oh Gosh! Guy man motar nan fa ya ƙare." Cikin takaici Sans ya ce, "Damn it! A tsakiyar dajin nan da babu giccin kowa ne mai zai mana haka?" "Ka dai gani ai." "Guy wats the solutuon?" "Don't really know abokina. Sai dai ko in kira Yax ya ɗauko jarka ya siyo ya kawo mana. Idan ba haka ba za mu shekara a nan, ba tare da kowa ya gitta ba. Kuma ga shi Saleem ya ce zuwa magrib za ka koma. Likitan ƙashin ya zo. Duk da dai ka samu sauƙi sosai, amma dai yana da kyau a ƙara tabbatar da lafiyarka." "Haka ne. Just give him a call to. Allah sa akwai kuɗi a hannunshi." "Ameen." Bobby ya faɗa, haɗe da zaro wayarshi daga jikin chaji yana mai ƙoƙarin kiran Yax ɗin. Kusan mintina arba'in suka ɗauka a wurin, kafin Yax ya iso, suka fita da nufin zuba mai a motar. Wani mahaukaci ne suka gani yana tinkaro inda suke, hakan ya sa suka firgita su duka, suna ƙoƙarin guduwa saboda yadda yake ƙara tinkaro su. Duhu ya fara a daidai lokacin, sai hasken wayoyinsu da suka dalle mahaukacin, wanda ya iso daf da su. Ido buɗe suke ƙare mishi kallo su duka ukun, kallon yadda kamanninsa suka zo ɗaya da Sans, babu ko bambanci. Sake kallon Sans suka yi Bobby da Yax, sannan suka sake dalle mahaukacin, don su sake tabbatarwa. Shi kanshi Sans ɗin mamaki yake. Tunda yake a rayuwarsa bai taɓa ganin tsananin kama irin wannan ba. *** Misalin ƙarfe sha biyu na dare ne Mama na zaune falo ta ji sallamar mace. Amsa sallamar ta yi tare da ba ta izinin shigowa cikin falon. Bayan ta zauna ne suka gaisa, duk da cewa Mama ba ta san matar ba, amma hakan bai hana ta sakar mata fuska ba. "Ya su Maryama? Ko ana makaranta?" "Maryama na ɗaki. Maryama!" Mama ta ƙwala mata kira. Da hanzari Maryama ta share hawayen nata, sannan ta fito cikin wani taku a nutse, da mutuwar jiki a tattare da ita. Murmushi ta saki a lokaci guda ganin wacce ta zo ɗin, zaune bisa kujera. Bayan ta ƙarisa shigowa ɗakin ta zauna ƙasan matar, haɗe da faɗin, "Umma ashe ke ce." Ta saki sassanyan murmushi. "Ni ce fa da kaina Maryama. Kin gan ni da rana tsaka ko? Ya na same ku?" "Lafiya lau Umma." Maryama ta juya ga Mama, ta ce, "Mama ita ce Umman Amrah. Dama na faɗa miki za ta zo ai." Faraa sosai a fuskar Mama ta ce, "Allah sarki! Ai ban gane ki ba." Umma ta ce, "Haka ne. Ko ranar walimarsu ba mu samu damar gaisawa ba. Yau ai ga ni na zo har gida." "Mun kuwa ji daɗi ƙwarai da gaske." Mama ta fada. Ta kalli Maryama ta ce, "Maryama kawo mata drink ko. Abinci ma na daf da sauka ai." Bayan Maryana ta miƙe ta ce, "Ehh Mama. Miya ce kawai ba ta ƙarisa dahuwa ba. Bara na kawo drink ɗin." Ta doshi hanyar Kitchen, tana mai jin wata nutsuwa sosai a tattare da ita. Damuwar da take ciki na ɗan raguwa, duk da dai akwai ta ɗin fanjam a cikin zuciyarta. Lemon five alive na roba ta sako guda biyu a plate, sannan ta ɗora cup a kai, ta nufi dawowa falon. Fira ta tarar Mama da Umma suna yi, tamkar dama can sun san junansu. A gaban Umma ta ajje, sannan ta koma kan kujera ta zauna, tare da faɗin, "Umma don Allah ki sha lemu kafin a gama abinci." Ɗaukar lemun ta yi Umma, ta fasa ta zuba kaɗan a kofi ta sha. Bayan ta shanye ne ta ce, "Ina Annur ɗin yake?" "Yana can ɗakin. Mu je ko?" Maryama da Mama suka miƙe, Umma ma ta miƙe. Sai da ta fara rufo ƙofar falon don kar a bar shi haka babu kowa, sannan suka nufi ɗakin da Modu yake, Maryama a gaba sai su Umma biye da ita. A zaune suka same shi, yana ta faman jeren alphabets, sai ha haɗa sunan Amrah da Maryama ta koya mishi, sannan ya haɗa sunanshi, sai kuma na Maryama a gaba. Kallonshi Umma ke yi cike da mamaki. Tabbas babu ko tantama Annur ne wannan. Real Annur, na Amrah. Ido buɗe suka ƙarisa shigowa cikin ɗakin, suna kallonshi. Ganinsu da ya yi ne ya sa Modu murmusawa, yana faɗin, "Maryama kin gani na iya? Kalla ki ga. Ga Amrah, ga Annur, ga ki." Ya saki murmushi yana gwada musu jeren da ya yi. Idonshi bai ankare da Umma ba har sai sadda Maryama ta mishi nuni da ita. Take gabanshi ya hau faɗuwa, ya ringa nuna ta da yatsa, bakinsa ya gaza furta komai. 'Hakan na nufin ya gane Umman Amrah kenan?' Maryama ta tambayi kanta. Da alama ana samun nasara, ana samun ci gaba sosai. Tunda ga shi har ya fara tunowa da wasu abubuwa na rayuwarshi. Ya fara tunowa da wasu mutanen da suka dangance shi. "Ka san ta ne?" Maryama ta gaggauta tambayarshi, tana ƙura masa dukkanin idanuwanta. "Ni ma ban sani ba. Kin san ni?" Ya tambayi Umma. "Ƙwarai da gaske kuwa Annur, na san ka, farin sani ma kuwa. Ni ce Umma, Umman Amrah. Ka tuna ni?" Dafe goshinsa ya yi alamar tunani, kafin ya ce, "Idan kin san ni to ni ma na san ki." Ya saki dariya har da tafa hannuwa. Dariyar suka yi su ɗin ma. Amma dai duk da haka akwai alamun ya ɗan tuna ta, ko ma dai yaya ne. Sun jima a ɗakin Umma na masa firar Amrah, da surkulle da sokana dai yake ɗan amsa mata, wasu abubuwan kuma idan ya yi tamkar mai hankali, sai dai kuma a take sai sako shirme, wanda zai tabbatar da cewa shi ɗin mahaukaci ne ba mai hankalin ba. Miƙewa Umma ta yi, ta ce, "Bari in ƙoƙarta tafiya, lokacin dawowar Mallam gida ya kusa. Kar ya dawo bai same ni ba." Mama ta ce, "Aikam Umman Amrah babu inda za ki tafi sai kin ci abinci. Ai ina jin ma ba zai rasa ƙarisa dahuwa ba. Maryama je ki bincika." Suka fita ɗakin a tare. Sai da Umman Amrah ta ci abinci ta yi sallar la'asar sannan ta tafi. Da godiya suka rabu da Maryama, tana mai tsananin jin daɗin kalaman Umman Amrah, na cewa za ta rinƙa zuwa akai akai, har zuwa lokacin da zai samu lafiya ya koma asalin gidansu. Da yamma Mama da Maryama suna zaune a falo, bayan Muhammad ma ya dawo daga Islamiyya yana ta musu zuba, wayar Mama ta ɗauki ƙara. Daga jikin chaji Muhammad ya ciro ya miƙo mata, ta duba ta ga Abba ne ke kiranta. Da sallama ta ɗauki wayar, sai dai a maimakon ta ji Abba ya amsa sallamar, akasin haka ta samu. Cike da masifa ya ce, "Na turo Mallam Ya'u yanzu yanzun nan ya zo ya ɗauko ku. Ku zama cikin shiri, zai kawo ku gidan Yaya Imrana ne. Ina nufin har da Maryama." Bai jira ya gama sauraren tambayar da Mama ke masa ta lafiya? Ba, kawai ya datse wayarshi. Cike da mamaki ta kalli Maryama, fuskarta na nuna zallar damuwa, ta ce, "Wai mu shirya yanzu Mallam Ya'u zai zo ya tafi da mu gidan Yaya Imrana. Allah dai Ya sa lafiya." "Ameen." Maryama ta faɗa baki ɗaya jikinta babu ƙwari. Miƙewa ta yi babu kuzari ta nufi ɗakinta, ta ɗauko dogon hijabinta ta saka, sannan ta zauna da wayarta a hannu, tunani da fargaba sun taso ta gaba, tana son sanin haƙiƙanin dalilin wannan kiran na gaggawa da aka musu. Bayan kamar mintina sha biyar sai ga Mallam Ya'u ya iso. Da sallama ya shigo ya sanar musu cewa su fito su tafi. Haka suka mimmiƙe jiki babu ƙwari, shi kanshi Muhammad fargabar abin da zai iya faruwa ce ta ɗarsu a zuciyarsa. Fatan samun nasara kawai yake, har suka isa gaban motar. Muhammad ne a gaba, sai Maryama da Mama a bayan motar, bayan sun tabbatar ma mai gadi cewa ya kula da Annur da ke ciki, ba za su kulle ba gudun samuwar wata matsalar. Da isarsu aka buɗe musu babban gate ɗin gidan. Gida ne babba mai matuƙar girma, wanda ke ƙunshe da parts kusan guda biyar. Bayan sun faka motar ne suka firfito, dreba kawai suka bari a ciki, su kuma suka ƙarisa part ɗin kawu Imrana, da hasashen a can za su samu Abba. A babban falon suka yi sallama. Ɗaki ne mai girma, wanda ya ƙawatu da kayan alatu. Sanyin AC duk ya gama garwaye ɗakin, ga wani irin ni'imtaccen ƙamshi da ke tashi ta kowacce kusurwa. Tsit ɗin da suka samu a ɗakin ne ya matuƙar ƙara razana su. Ga Abba da Kawu Imrana jere bisa 3 seater, sai Deedah zaune a ƙasa, ya sunkuyar da kansa. Kawu Imrana ne ya amsa sallamar, haɗe da sakar musu murmushi, yana mai basu izinin ƙarisowa ciki. A ƙasa Maryama da Muhammad suka jera, suka gaishe da kawun nasu, yayin da Mama ta zauna can nesa da su, bisa 1 seater. "Sannunku da zuwa Hajiya." Kawu Imrana ya ce da Mama, a lokacin da take gaishe shi. "Yauwa Yaya. Allah dai ya sa lafiya, mun ji kiran gaggawa..." Tun ba ta rufe bakinta ba Abba ya fara masifa, "Ina fa lafiya. Ƙaramar yarinya kamar Maryama tana neman miyar da mu wasu shashashu, wanda ba su san abin da suke ba. Wato ita har ta yi ƙamarin da babu kunya za ta nunar da ba ta son Ahmadu ko? To wallahi ba ta isa ba! Ke ba ki isa ki baɗa mana ƙasa a idanuwa ba. Yaran yanzu sam! Ba ku san arziƙi ba." Da hannu Kawu Imrana ya dakatar da shi, yana murmushin dattako ya ce, "Ya isa haka Balarabe. Ba a haka ai. Ni yanzu duka ba wannan ne dalilin da ya sa na tara ku ba. So nake na ji bayani daga bakin Maryama." Ya juya ya fuskance ta, ya ce, "Ƴata kina son Ahmad ko bakya son shi? Ko kaɗan ba na so ki ji kunya ko kuma nauyin faɗi, feel free and tell me, babu wanda ya isa ya miki auren dole. An wuce wannan zamanin ai tunin duniya. Dama tun farko na ji daga bakin Ahmad ɗin ne, kuma shi da kanshi ya faɗa min irin shaƙuwar da take tsakaninku. Ki faɗa min gaskiya, tun daga cikin zuciyarki." Kuka ne ya kufce ma Maryama, ta sadda kanta ƙasa, tana mai rasa dukkanin nutsuwarta. Ta ma rasa me za ta faɗa. Shin ta yaya za ta iya buɗe bakinta a gaban Kawu Imrana da kuma shi kanshi Deedah ɗin ta ce wai ba ta son shi? Abu dai da kamar wuya. Ba ma za ta taɓa iya wannan ta'asar ba. Ita ba ma ta san ta ya akai har zancen ya fito ba, cewa wai ba ta son Deedah. Cikin kwantar da hankali Kawu ya ce, "Ba na so ki cuci kanki ƴata. Wallahi na miki alƙawari zaɓinki za ki aura. Ƙin amincewa da auren Ahmad kuwa ba zai taɓa shafar dangantakarmu ba. Da a ce sai an yi a zo zumunci ya ɓaci, ai gwara tun wuri a tarbi abun." Cikin ƙarfin hali take son shanye kukanta. Ta saka dukkanin hannayenta tana sharewa hawayen, sai dai kuma wasu sabbi ne ke saukowa. Satar kallon Deedah ta yi, ta ga yadda ya baza dukkanin idanuwansa yana kallonta, yana mai son jin me za ta faɗa. Da shessheƴa ta fara magana, "Kawu, Abba, ku gafarce ni, ba na son a ce na zama silar ɓacin ranku. Amma wallahi ko kaɗan ban taɓa son Yaya Deedah da aure ba. Irin soyayyar da nake ma Hammad ƙanina ga shi nan, irinta nake ma Yaya Deedah. Ku yi haƙuri don Allah, amma a bar kowa da zaɓinsa." Cikin zafin nama Abba ya taso da niyyar ya wanka mata mari, sai dai Kawu ya riga shi isa gare ta, ya san zuciyar ɗan uwanshi, ya san cewa dukan nata zai yi dama. Riƙe masa hannuwa ya yi, ya ce "A kan me za ka dake ta? Don kawai ta faɗi ra'ayinta? Kar mu yi haka da kai Balarabe. Ko akwai wanda ya yi maka dole a sadda za ka yi aure? Babu. Haka ni ma babu wanda ya min dole. Matana uku a halin yanzu, babu wacce aka haɗa ni da ita, ko kuma aka mana auren dole. Duka auren soyayya ne. Saboda haka ƴata ma ban ga wanda zai mata dole ba. Wanda duk take so shi zan aura mata." Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke Maryama. Tana jin wani irin daɗi a cikin zuciyarta. Damuwarta na ragewa, saboda jin kalaman Kawu. Sai dai kuma so ɗaya da ta haɗa ido da Abbanta ba ta sake marmarin kallonshi ba. Tsantsar jin haushinta da yake kawai ta iya hangowa a cikin ƙwayar idanuwansa. "Yanzu Yaya goyon bayan wannan shashashar yarinyar za ka yi? To ni dai sam! Ba da yawuna ba. Ahmad Deedah na ce ta aura, ba kowa ba." Murmushi ya yi Kawu. Ya dafa kafaɗar ɗan uwanshi, yana faɗin, "Ashe dai har yanzu baƙar zuciyar nan da na san ka da ita tana nan. Sai yaushe ne za ka san ka girma Balarabe? Ka rufa wa kanka asiri ka rage wannan halin, ko kaɗan ba hanyar ɓullewa ba ce." Gyaɗa kansa ya yi, ya ce, "To idan ba ki auri Deedah ba uban wa za ki aura? Na ce uban waye wanda kike so?" Bakinta kyarma yake, ta gaza furta komai, hankalinta na daɗa tashi. Kallon Mama take tana neman taimakonta, tana son jingina a jikinta ko za ta ɗan samu nutsuwa, amma ina, Mama ma harararta ta yi, tana mai tsananin jin haushinta. Hammad ne ya riƙe mata hannun dama, yana mai ɗaga mata kai alamar ba ta ƙwarin guiwa, haɗe da sakar mata ɓoyayyen murmushi, wanda a tsakaninsu kawai za su san ya yi shi. "Wallahi kin ji na rantse aure zan miki. Ko ki fiddo miji nan da sati biyu ko kuma in nemo duk wanda nake so in haɗa ki da shi. Wanda bai yi sharar masallaci ba ai ya yi ta kasuwa." Tsananta duka kawai gabanta ke yi. Wani irin raɗaɗi take ji a cikin zuciyarta. Sauyi kawai take gani daga wurin Abbanta. Me ya sa zai mata haka? Shin kanta farau irin haka? "Da ke nake magana!" Ya zaro mata idanuwa, ya ma ƙi sauraren Kawu da ke dakatar da shi. "Ka yi haƙuri Yaya. Amma na riga da na rantse. Wallahi aure zan mata, cikin kwanakin nan ba ma da nisa ba. Ba dai ni za ta kunyata ba? Kar ma ka yi ƙoƙarin dakatar da ni. Don Allah." "What are you still doing Bala? Kana ɗaukar aure kamar wani abun wasa. Ta ya za ka ce aure za ka mata, babu wani binciken kirki?" "Ita ta ja komai Yaya. Don haka ke nake sauraro. Waye shi, kuma ɗan gidan waye? Ban damu da wadata ko rashinta ba. Ke nake sauraro!" A iya wannan lokacin kam tsoro ya gama mamaye dukkanin gaɓoɓin jikinta. Yana zagaya duk jini da jijiyoyinta. Kallon da yake mata ne ya sa ta ƙoƙarta tattaro magana, ba tare da ta san me take faɗi ba, ta ce, "Annur nake so!" *** *You know what? 4k words na muku yau. The most longest page since after Sallah. Fatan kun ji daɗinshi sosai.* *Readers, ya kuke ganin wannan al'amarin? Shin Abba ya kyauta kuwa wannan gaggawa da ya saka a auren Maryama? Zai amince da zaɓinta, duk dayake cewa Annur ɗin mahaukaci ne? Ta ya auren mahaukaci da mai lafiya zai yiwu? Idan har ya amince ɗin ma, a haka za ai aure babu danginshi ko ɗaya? Kodai za su miyarshi gida ne sannan a yi auren?* *Amsoshin tambayoyin suna ga alƙalamin marubuciyar, sannu a hankali za ta warware mana dukkan tambayoyin.* *Mutanena masu mutunci kuna ina? Kun ga dai na karkata na rubuto muku dogon shafi mai mutunci. Fatan kuma za ku karkata hannayenku zuwa ga ƴar tauraruwar nan domin ku kankaro min mutunci ni ma.😘😀* *Ghosties kuma masu kama da cartoons, ku ci gaba da laɓe. Insha Allahu wayoyinku hucking za su rinƙa yi muku daga yanzu.😏* Thanks all Pinky durling💞 RAZ 2 [9/8, 12:49 AM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 5⃣8⃣ Wattpad: Princess Amrah *** "Wurin Amrah nake so ku kai ni. Kullum sai na sha fama da Dadyna da Momyna kan cewa su kai ni inda Amrah, amma sai su ce da ni wai Amrah ta mutu, ba zan sake ganinta ba. Ni kuwa ta kufto na gudo ba tare da sun sani ba. Ai za ku taimaka min ko?" Dariyar yaƙe yake, amma kuma ruwan hawaye na sauka a bisa kumcinsa. Sai famar sauke ajiyar zuciya yake. Sosai suke mamakin wannan mahaukaci. Muryarsa da duk yanayinsa iri ɗaya ne da Sans, ba su da bambanci. To waye wannan? Kuka ya fasa mai ƙarfi. "Don Allah ku ma kar ku ce min Amrah ta mutu. Kar ku ce ba zan sake ganinta ba. Wallahi Amrah nake so! Ita nake ƙauna, da ita nake da burin ci gaba da rayuwata." Ya dafe kansa, tamkar wani mai cikakken hankali. "Ina ne gidanku, kuma su waye iyayenka?" Sans ya yi ƙarfin halin tambayarsa, duk da mamaki da ya gama garwaye dukkan saƙon da ke cikin zuciyarsa. "Ban sani ba ni ma. Dady da Momy su ne iyayena. Amma ban san su ba, ban san gidanmu ba." "To kar ka damu. Za mu kai ka inda Amrah. Za ka bi mu dai ko?" Kansa ya ɗaga da sauri, har yana cin tuntuɓen magana, ya ce, "Zan bi ku. Ku kai ni wurin Amrah, na tabbata ita ma tana can tana jira na mu yi aure." Mamakin abin da Sans ɗin ya faɗa ne ya wanzu a zuciyar Bobby. Ya kalli abokin nashi yana son yin magana, amma ya ɗaga masa hannu, alamar kar ya ce komai. "Kamar yadda kuke mamaki to ni ma haka nake yi. Kamar yadda ba ku san shi ba ni ɗin ma haka ban san shi ba. Haka kawai jikina yake ba ni something will happen, alkhairi ba sharri ba. Ku duba yanayin fatarsa, alamun ya ji hutu kenan. Da kuma suturar da take jikinsa, duk da kasantuwarsa mahaukaci, amma tsadaddu ne. Don haka na yanke hukuncin mu tafi da shi. Kuma koda ma a ce ba haka ba, abu ne mai matuƙar mamaki, mutum ya haɗu da mai kamanni sak irin nashi, ko kaɗan babu bambanci. Ba na jin zan iya tafiya in bar shi, har sai na gama bincike a kansa." Jinjina kansa ya yi Bobby. Ya ce, "Good thinking. To amma yanzu ya za mu yi da shi? Tunda ba gida za mu nufa ba." "Wannan mai sauƙi ne. Yax ya tafi da shi a kan mashin. Mu kuma sai mu hanzarta tafiya asibitin." "Amma kamar da wahala fa mahaukaci ya hau mashin ba tare da mai kula da shi ba. Kuma inda na san da haka da sai in ce ya zo da napep ai. Ko kana ga babu komai?" Sans ya ce, "Gaskiya ka faɗa kai ma. To ko za ku tafi da motar can gida ni sai in tafi asibiti a mashin ɗin? Na ga ai ba daɗewa zan yi ba." Bobby ya ce, "Ƙafarka fa. Za ka iya tuƙin mashin babu matsala?" "Babu matsala Guy. Idan ma akwai, I'll give you a call." Bobby ya ce, "To shi kenan abokina. Bari mu wuce." "A kula da shi sosai Guy. A ba shi abinci ya ci. A masa duk dabarar da ta dace kafin in dawo. Idan ka ji ni shiru ka kira ni." Da haka suka rabu, su Bobby suka juya baya domin komawa gidan gonarsu, yayin da Sans ya haye bisa mashin ya kama hanyar shiga cikin gari. * Waya yake cike da ƙunci da damuwa. Jikinsa har karkarwa yake, yana faɗin, "Inspector ban san sadda ya fita ba. Ba ni kaɗai ba, dukkan ƴan gidan ma babu wanda ya kula da fitarsa. Tun sadda ya kamu da ciwon nan yake attempting guduwa ake kama shi, daga ƙarshe ma aka fidda masa ɗaki guda haɗe da ɗaure shi, aka kuma datse ɗakin. Ta yadda dai muke zargin fitarsa, wata ƙila ko sadda aka kai mishi abincinsa na rana ne wanda ya kai mishin ya manta bai rufe ƙofar ba. Tunda dama idan an kai mishi abincin kwance shi ake yi, har sai ya cinye sannan a koma a ɗaure shi, amma sai an datse ɗakin. To kuma bayan ya gama cin abincin ne aka tarar ba ya nan. Inspector don Allah a taimaka mana, wallahi daga ni har mahaifiyarsa hankalinmu a tashe yake. Ba mu san inda Annur zai faɗa ba. Ba mu san a rayuwar da zai afka ma ba." Sai a nan ya ci burki. Yana sauraron abin da inspector ɗin ke ce mishi. "Ka cire damuwa daga ranka Pharm IA. Insha Allahu Annur zai bayyana. Za mu same shi a yau ɗin nan." "Ina fatar hakan Inspector. Allah Ya bayyana shi. Na gode ƙwarai. Sai na ji ka." Ya tsinke wayar daga nan, yana mai juyawa ya fuskanci Matarshi da ke ta famar kuka riris, ya ce, "Ki yi haƙuri ki daina kuka. Da yardar Allah zai bayyana, cikin ƙoshin lafiya." Shessheƙar kuka take, ta ce, "Allah tabbatar mana." Haɗe da share hawayenta, tana sharewa wani na daɗa saukowa. Da yamman aka barbaza ƴan sanda domin neman Annur. Duk wasu tituna da ke cikin garin Katsina sai da aka watsa ƴan sanda. Daji daji haka suka rinƙa shiga. Saboda kuɗi ne masu mugun yawa Pharm IA ya tura musu. * Gudu yake sosai Sans, sai dai ya taka burki, a daidai isar shi wani check point, inda tun daga nesa ya hangi faskeken hoto irin nashi, sai dai ba shi ɗin ba ne. Akwai layin motoci da mashina a gabanshi, saboda daidai junction ne. Hakan ya ba shi damar karanto rubutun da ke manne jikin hoton, cewa ana neman Annur Iqra Al-Hussein, mahaukaci ne, za a gan shi da kaya kala kaza, ya fita ne da misalin ƙarfe uku na rana. Hasken traffic ne ya dalle rubutun, har Sans ya kai ƙarshe a karanta shi. Mamaki yake sosai, take zuciyarsa ta kitsa mishi abin da zai yi. Ba dai mahaukaci ba ne? Na san abun yi. Ya lallaɓa ya yi kwana, ya bi one-way har sai da ya isa u-turn, sannan ya ci gaba da zura gudunshi, da nufin komawa gidan gona. *** Cikin mamaki Abba ya kalli Maryama, bakinsa na rawa ya ce, "Wane Annur ɗin kike magana? Kar dai ki ce min wannan mahaukacin." Kai kawai ta ɗaga ma Abba, tana zubda hawaye sosai. Ita kanta Mama sai da ta sha mamaki. Deedah ma kallonta yake ƙyam, yana nazartar yanayinta. Bai san komai da ke wakana game da Annur ba, kawai dai ya san cewa Annur ya zama riƙaƙƙen ɗan iska; manemin mata kuma mashayi. Amma don me Maryama za ta zaɓi wannan tuƙururun ɗan iska a matsayin abokin rayuwarta na har abada? Dama dalilin da ya sa ta taɓa tambayarsa Annur kenan? Gyaɗa kansa ya yi, yana jin ba zai iya yin shiru ba, dole ya yi magana a wannan gaɓar. "Abba ku gafarce ni, zan ɗan yi magana." Ya juya ya kalli Maryama, ya ce, "Maryama ki rufawa kanki asiri, ba wai don kishi ko wani abu ba. Ba kuma ina miki buƙulun auren wanda kike so ba ne. Amma fa bai cancanke ki ba. Annur ba ya sahun mazajen da ya kamata a ce kin aura. Me ya sa? Maryam don me za ki tsaida Annur, duk tarin mazajen da ke duniyar nan? Ki dai canza tsari, ki canza zaɓi, wallahi ba ki cancanci auren fasiƙin namiji irin Annur ba." Yana kaiwa nan ya dakata. Yana sauraren abin da zai biyo baya. Kawu Imrana ne ya yi gyaran murya, ya ce, "Duk wani halin hauka da yake ciki, mai sauƙi ne, mafi tsananin dai wannan halayen nashi da Ahmad ya faɗa." Mamaki sosai Deedah ke yi. Hauka? Ya tambayi kanshi. Kenan Annur ya koma ruwa? Ya taɓa sanin sadda ya haukace, wanda tun bayan nan ne ya warke baki ɗaya ya canza halayenshi. "Maryama. Dole za ki canza tsari. Duk da na miki alƙawarin aura miki duk wanda kike so, hakan ba yana nufin wai zan yarda ki auri kowanne irin mutum ba ne. So nake na gina rayuwarki. Ki auri mutumin kirki, wanda zai kyautata miki, ki ji daɗinsa, ko muna raye ko kuma ba mu raye." Cikin ƙoƙarin shanye kukanta ta ce, "Kawu, wanda Yaya Deedah ke magana fa ba shi ba ne Annur. Ainahin Annur ɗin yanzu haka yana gidanmu, cikin halin taɓin hankali..." Ta kwashe komai da ta sani, tun daga farko har ƙarshe, a taƙaice ta sanar da shi. Abba da ke zaune bai musa ba, saboda ya san yadda komai ya faru. "Kawu wallahi in dai don hauka ne, ni na amince a hakan zan aure shi. Adduarku kawai muke da buƙata." Gyaɗa kansa ya yi kawu Imrana. Ya ce, "To shi kenan ai. Tunda dai kin zaɓi hakan, kuma ya kasance mutumin kirki ko kafin haukan nasa, babu komai. Allah ya tabbatar mana da dukkanin alkhairanSa. Yanzu ai dole za a kai shi gidansu ko? Tunda ai ba zai yiu ai aure ba tare da wani nashi ba." Ɗago kanta ta yi, ta ce, "Wannan mai sauƙi ne Kawu. Akwai ƙawata Jiddah, Mamanta ƙawar maman Annur ce, zan mata magana, mu nemi kawunshi mu yi maganar, in masa bayanin komai, sannan in haɗa ku. Ba na son Annur ya koma gidansu a cikin ƴan lokutan nan, saboda wancan fasiƙin da ke zaune gidan a matsayin Annur ɗin, kar ya ɗauki wani mummunan mataki a kanshi." "Babu damuwa to. Ki dage da addua. Insha Allahu komai zai zo yadda ake so. Ku tashi ku tafi kawai, dare na yi." Godiya sosai Maryama ta masa. Zuciyarta na mata daɗi sosai, ta ƙara da faɗin "Kawu don Allah ka nema min gafarar Abba. Ya yafe min. Wallahi ba haka na so ba ni ma, ni kaina ban san yadda aka yi ka san wannan zancen ba." Murmushi ya saki kawun, ya ce, "Kar ki damu. Fushi ne ya yi, kuma na tabbata zai yafe miki. Ku je kawai. Hajiya sai da safe ko?" Jiki a sanyaye Mama ta ce, "Mun gode ƙwarai Yaya. Sai Allah ya tashe mu lafiya." Ba su ko shiga sauran parts ɗin gidan sun gaisa da matan nashi ba, suka zarce inda motarsu take, Mallam Ya'u ya tayar, suka nufi gida. * Da isarsu gida ta faɗa bisa kujerar falo tana kuka sosai, kukan da ita kanta ta rasa gane ko na menene. Kuka sosai take, mai haɗe da ƙara da shessheƙa. Ji ta yi an dafa ta. Ba ta ɗago kan nata ba bare ta nemi sanin wanda ya dafa ta ɗin. Sai ƙarfafa kukan nata ma da ta yi. Muryarshi ta ji ya ce, "To ai kuma ta kuka ta ƙare ko Yaya? Ina don za a miki auren dole ne ya sa kike kuka? To ai an fasa. Kawu da kanshi ya miki alƙawarin ba ki auren wanda kike so. Dama kuma ai na miki wannan alƙawarin ko?" Sai a sannan ta ɗago fuskarta da ta gama kumburewa don kuka. Idanuwanta baki ɗaya sun rine, sun zama jajaye. "Hammad dole ne na yi kuka. Yanzu da wane ido zan ci gaba da kallon Kawu? Na rasa ta yadda aka yi ya san cewa ba na son Yaya Deedah, tunda dai na tabbata Abba ba zai taɓa faɗa masa ba, kamar yadda ya ce ɗin. Na rasa a wanne babi zan saka rayuwata a daidai wannan lokacin. Shin farin ciki ne ko kuwa baƙin ciki?" Guntun murmushi ya yi Hamnad, haɗe da sassauta muryarsa, ya ce, "Ni ne nan na kira kawu ɗazu da safe." Ya kuma sakin sassanyan murmushi, wanda ke ƙara ƙawata kyakkyawar fuskarsa.  Cike da mamaki ta kalle shi. "Kai ne?" Kai ya jinjina mata. Sai yanzu ta gama gane komai. Saboda ɗazu da rana Mama ta ɗauko wayarta ta ga sunan Kawu a dials ɗinta. Har ta tambaye ta ko ita ta kira shi? Amma ta ce ba ma ta ga wayar tata ba tun safe. Mama ta ce to ƙila Abba ne ya kira, duk da dai ba ta tsammanin shi ɗin ne. Muhammad ya buɗe bakinsa ya ce, "Abin da ya faru shi ne, bayan mun gama gaisawa da Kawu, ya nemi sanin dalilin da ya sa na kira shi. Cikin rawar murya na ce, "Kawu dama so nake in faɗa maka wani abu. Ka kuwa san cewa Yaya Maryama ba ƙaunar Yaya Deedah take ba? Wallahi Kawu yanzu haka tana can tana kuka. Damuwa ta taso ta gaba, tun daga jiya ba ci ba sha. Kuma Abba ya ce ba ta isa ba! Dolenta ta auri Yaya Deedah ko tana so ko ba ta so. To Kawu ni kuma ba na so a ma Yaya Maryama auren dole. Ina son ta fita daga cikin wannan damuwar da take." Kawu Ya yi shiru jim! Kafin ya ce, "To kai waye ya faɗa maka haka? Ita Maryamar ce ta saka ka ka kira ka sanar min?" Na ce, "Ko kaɗan Kawu, Yaya Maryama ba ma ta san zan kira ka ba. Ita dai kawai ta sanar da ni cewa ba ta da ra'ayin auren Yaya Deedah. Kamar yadda ta ɗauke ni ɗan uwanta na jini to haka ta ɗauke shi. Kuka kawai take ta famar yi tun jiya, har wayewar garin yau. Ni Kawu abin da ma ya fi ba ni tausayi shi ne, hatta da gaisuwarta yau Abba bai amsa ba. Kawai don ta nunar da ba ta son Yaya Deedah da aure, shi kuma ya ce ba zai iya tinkararka da wannan zancen ba." Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke, ya ce, "To shi kenan Muhammad. Insha Allahu za a duba, za kuma a yi duk abin da ya dace. Kar ka faɗa ma kowa ka ji? Ni ma babu wanda zai ji daga bakina. Na maka alƙawari." Daga nan na mishi sallama sannan na tsinke wayar, na lallaɓa na dawo da wayar zuwa ɗakin Mama." Ba ta san sadda ta saki murmushi ba Maryama. Ta miƙa masa hannu suka kashe, ta ce, "Good and talented boy. Who teach you all these?" Murmushin ya yi shi ma. Ya ce, "My brain." "I have trust on it." Ta kuma sakar masa murmushi. Tana jin ƙaunar ƙanin nata na daɗa yawaita a cikin zuciyarta. Wani abu sai jininka. Ranar naka kuwa sai naka. Yanzu idan ba Muhammad ba waye zai iya yi mata haka? Don ma dai yaron yana da ƙarfin hali. Yadda suke girmama Kawu Imrana, ko ita da take babba ba za ta taɓa tunanin ta tinkare shi da maganar ba, amma shi har ya yi wannan tunanin. "Around of applause for yourself." Ta faɗa tana taya shi tafa ma kanshi. Mama da tun ɗazu take tsaye tana saurarensu mamaki ya gama kashe ta. Har ga Allah zuciyarta ta gama tunzura ta da ta yi fushi da ƴar tata, saboda kunyata su da ta yi. Sai dai yanzu ta saduda, ta roƙi ƴarta a cikin zuciyarta, cewa ta yafe mata, ta nemi ɗaukar alhakinta ba tare da haƙƙinta ba. Ashe ita kanta ba ta san abin da ke wakana ba, aikin Muhammad ne duka. Gyaɗa kanta ta yi tana mai share dukkanin ƙwallan da suka gama kwarara bisa fuskarta. Soyayyar ƙani da yayarsa ta burge ta, yadda ƙaramin yaro ɗan shekara goma sha biyu kamar Muhammad ya ɗauki damuwar yayarsa a matsayin tashi. Ya gusar mata da damuwarta ba tare da shakkun komai ba. Lallai ƙauna ta yi ƙauna. Shaƙuwa iya shaƙuwa. Ɗakinta ta nufa domin gabatar da sallar magrib, da kuma ta isha'i da ake kan kiranta. Miƙewar ta yi ita ma Maryama, ta ce da Muhammad za ta fara shiga ɗakin Annur ta ga lafiyarsa, kafin ta nufi nata ɗakin ta yi sallah, shi ɗin ma ya je ya sauke tashi. A zaune ta same shi, yana aikin wasa da alphabeat kamar yadda ya saba kodayaushe. "Ya Noor barka da dare." Ta furta bayan ta ƙarisa shigowa ɗakin. "Me ya sa kika yi kuka?" Kawai ta ji ya faɗa, bayan ya gama nazartar yanayin fuskarta. Saurin share fuskarta ta yi, da ƙirƙiro murmushi ta ce, "Waye ya faɗa maka na yi kuka? Ni ban yi kuka ba. Ciwon ido ne fa nake yi." "Amrata ba ta ƙarya. Ba ta ɓoye min dukkanin damuwarta. Ki yi ƙoƙarin zama kamarta." Tamkar ba shi ya yi maganar ba, ya ci gaba da wasan shi. Kallon shi kawai take, mamakin kalamansa take sosai. Wurin zama ta nema, ta ce, "Ya Noor magana za mu yi." Shiru ya mata, ba tare da ya furta komai ba, sai dai murmushi kawai da yake saki. "Ya Noor, aure Abbana ya ce zai min." Ɗago kansa ya yi cikin kiɗima, idanuwansa a buɗe, ya gagara furta komai. "Ka san wa na ce masa zan aura?" Ba ta jira me zai ce ba, ta ci gaba da faɗin, "Na ce masa kai nake so, kai zan aura." Dariya ya saki mai nuna zallar nishaɗin da kalaman nata suka saka shi. Ta ci gaba da, "Za ka amince ka aure ni ko?" "Ehh mana. Ba na faɗa miki Amrata ta ce na aure ki a madadinta ba? Na ji daɗi, za a mana aure." *** *Na gaji. A yi haƙuri da wannan, tunda dai jiya na muku posting.* *Sannu a hankali na fara warware muku wasu abubuwa ko? Kun dai ga mahaukaci mai kama da Sans, wanda ba kowa ba ne face Annur. Haka kuma mun ga yadda ake nemansa ruwa a jallo, da kuma ƴan sanda da aka baza domin neman shi. To sai dai abin da ba mu gama sani ba, me ya sa Sans ya gaggauta guduwa ba tare da ya ƙarisa wurin ƴan sandan ba? Hakan na nufin yana da wani ƙudiri ne? Me kuke hasashe? Drop your comments.* *Masu mutunci kar ku manta dai, ku cika aikinku na kankaro mutunci.😀* Thanks all Pinky durling💞 RAZ 2 [9/8, 11:31 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 5⃣9⃣ Wattpad: PrincessAmrah *** Mamaki fal ya kama Bobby a lokacin da Sans ya gama yi masa bayanin abin da yake faruwa. "To me kake tunanin yi yanzu?" Ajiyar zuciya ya sauke Sans, ya ce, "Ina tunanin komawa gidansu a madadin mahaukacin da na ga an maƙala sunanshi Annur. Tunda dama ka ga nan ɗin da nake zaune ba a kowa nake ba. Ba zai yiu rayuwata ta dauwama a gidan gona ba, kuma a ƙarƙashinka. Nan gaba zan iya zame maka wani nauyi. Gwara dai tunda ga mafita ta zo, a sauƙaƙe kawai in koma gidan nasu, ba za a samu matsala wurin canje canjen halaye ba, tunda dai ka ga shi ɗin mahaukaci ne, da hauka ya baro gidansu." Hannu Bobby ya ba shi suka tafa. Ya garƙame hannun gam-gam yana faɗin, "Guy kai shege ne fa. Ka san hanyoyin ɓullewa da dama. Amma ka san me? Akwai wani Boka da nake zuwa wurinshi, duk sadda wata matsala za ta taso min. Kawai za mu je wurinsa, sai ya ɓatar mana da wannan mahaukacin, a masa kurciya koma ina ne ya tafi. Sannan kuma a kashe bakin iyayen nashi, kar su taɓa ɗago ka, kar kuma su taɓa yin shakku kan cewa Annur ɗin su ne ko ba shi ba ne? Kamar hakan zai yi ai ko?" Jinjina kansa ya yi da sauri Sans, ya ce, "Good idea. Yanzu yadda za a yi, a mishi dabara a raba shi da kayan jikinsa, su dawo a jikina. Sannan in fita cikin daren nan, ba na so a kwana. Ba kuma da yanayin hauka zan koma musu ba. Cikakken mai hankali zan koma, saboda kar abun ya yi tsayi, in rinƙa yin hauka saɓanin wanda shi ɗin yake yi, har wata maganar ta ɓullo, a samu matsala mai girma. Ko ya ka ce?" "Hakan ya yi daidai Sans." Ƴan yatsunshi biyu ya ɗora a laɓɓanshi haɗe da faɗin, "Shshshsh! Kar in kuma jin Sans a bakinka. Annur nake a yanzu." Ya ƙarisa maganar da sakin tattausan murmushi. "Amma fa guy har yanzu ina mamaki. Kodai asalinku twins ne wai?" "Kai share kawai. Kamanni ne kawai aka samu. Kodayake dai Aunty ta taɓa faɗa min cewa mu twins ne, amma ai ka ga ba a gari ɗaya ba ne. Kuma ainahin twin brother ɗina ya rasu tun sadda aka haife shi, kafin ma ni in fito duniya. So, ka daina wannan tunanin. Its just a coincidence." Kafaɗunsa ya ɗaga duka biyu Bobby, ya ce, "Shi kenan ai. Yanzu me ya kamata a yi?" "Kawai tare za mu tafi. Idan mun haɗu da ƴan sanda sai ka ce tsinto ni ka yi a galabaice, shi ne na ce ka taimaka ka kai ni gida. Idan kuma ba mu haɗu ba, kai tsaye mu ɗauki address ɗin gidan su Annur ɗin, mu nufi can. Na san me zan yi daga nan." Bobby ya ce, "Yadda ka ce a yi haka za ai. Sai dai kuma abu ɗaya." "Mene ne?" Sans ya tambaya. "Ba ka yi kama da wanda ya galabaita ba." Ya saki murmushi Bobby bayan ya yi wannan maganar. "Kar ka damu, na san me ya dace. Yanzu dai kai snapping gashinsa, yadda askin kanshi yake, daga nan idan ba mu haɗu da ƴan sandan ba sai mu samu mu nufi wurin mai askin nan ya miyar min irinshi. Idan kuma mun haɗu da su shi kenan. Na tabbatar in dan aski ba za su taɓa kawo komai a ransu ba. Nan da kamar kwana biyu ko uku sai mu je wurin bokan." "Guy kana tunanin daga tasowarka hauka za su bar ka ka fita ne? Ba na jin za a tama barin ka. Gobe da sassafe na maka alƙawarin zuwa wurin bokan da kaina. Zan mishi bayanin komai, duk yadda aka yi zan zo har gidan na sanar maka." Daga nan suka nufi Annur gadan-gadan, suka yi musayar kayan jikinsa, Sans ya miyar a nashi jikin, sannan suka kama hanyar tafiya. Sun ci sa'a kuwa ba su haɗu da check point ko ɗaya ba har suka isa wurin mai askin. Bayan an gama suka karanta address ɗin su Annur a wani round about da aka maƙala hotonshi. Gidan babu wahalar ganewa sosai, hakan ya sa ba su wani ɓata lokaci ba suka isa. A yanayin yadda Sans ya koma, tsaf za a iya cewa lallai Annur ne. Kominsu iri ɗaya. Askin kanshi irin na kan Annur ne. Dama kuma tafiyarsu da komai iri ɗaya ne. Ya ƙoƙarta miyar da kanshi tamkar wani galabaitacce, wanda ya tashi daga cutar hauka. A ƙofar gida Bobby ya faka motar. Ya zagaya ya buɗe ma Sans gefenshi, sannan ya tallabo shi a hankali yake taku, har suka isa bakin gate. Knocking ya yi har sau biyu, sannan mai gadi ya zo har da gudu-gudunshi yana faɗin, "Yi haƙuri fa, na ɗan zaga ne." Fuskarsa ta rikiɗe da mamaki lokaci guda, sadda ya haɗa ido da Sans. Idonshi a buɗe yake faɗin "Annur! Kai ne? Ina ka shige ana ta nemanka? Alhaji da Hajiya sun damu sosai da rashinka. Amma kwa na ji daɗi da Allah ya sa ka dawo lafiya. Ku shigo daga ciki Mallam." Bobby ya koma tamkar wani mutumin kirki. Mai gadin ya musu jagora har suka isa cikin gidan. A falo suka tarar da Hajiya Suhaila sai famar kuka take. Islam ma na yin nata, Pharm IA sai famar rarrashinsu yake. Sallama mai gadin ya yi, sannan Bobby ya biyo bayanshi har yanzu bai saki Sans ba. Zabura Pharm IA ya yi a daidai sadda ya ɗago kanshi ya ga Sans. Ido a buɗe yake faɗin, "Shi kenan ma, sai ku daina kuka ai. Ga Annur nan Allah ya taimake mu ya dawo, ko kwana ma bai yi ba, Allah ya dubi duminiyarmu." Ya saki faffaɗan murmushi, yana ƙarisa isowa a gaban su Bobby. Kama hannun Sans ya yi, yana faɗin, "Annur me ya sa ka tafi ka bar mu? Ka fa san cewa ba za mu iya rayuwa ba tare da kai ba. Mahaifiyarka ta shiga tashin hankali sosai, kalli ka ga, ƙanwarka ma kuka take tun daga sadda aka fahimci ba ka nan, ka bar gidan nan." Zaunar da shi Sans ya yi, ya ce, "Ku ɗaga hannunku ku gode wa Allah Alhaji. Domin kuwa a wani irin mugun daji na haɗu da wannan bawan Allah'n, a sadda motata ta dakatar da ni, sanadiyyar ƴar matsala da ta samu." Momy ta iso gaban Sans, ta dafa cinyoyinshi, tana kuka mai haɗe da murmushi, ta ce, "Na ji daɗi sosai da ka dawo gare mu Annur. Sannu ka ji?" "Ina Amrah take?" Ya buɗe bakinsa ya faɗa, duk da cewa bai san ko wacece ita ba, kawai dai ya fahimci cewa tana da matuƙar daraja a rayuwar wancan mahaukacin ne. Hajiya Suhaila ta ce, "Amrah ta rasu Annur, ka sani fa, sai dai idan mantawa ka yi." Kuka Sans ya fasa mai razanarwa da ƙarfi, tamkar da gaske ya shiga damuwar. Yana faɗin, "Me ya sa za ta tafi ta bar ni? Amrah na da matsayi mai girma sosai a zuciyata. Ina ji da ita fiye da duk tunanin mai tunani. Me ya sa za ta tafi ta bar ni? Me ya sa ta zaɓi barin duniya ta bar ni? Mutuwa ya za ki ma Annur haka? Da kin sani ki ɗauke ni ni ɗin ma, da zan fi samun sassauci a cikin zuciyata." Bai san ko wacece Amrah a rayuwar Annur ba. Bai sani ba, shin ƙanwarsa, yayarsa ce, ko kuma budurwarsa ce? Kodai matarsa ce? Shi ya sa ya yi wannan maganar, ya kuma dakata daga nan. Mamaki suke yi sadda Sans ya yi wannan maganar. A zukatansu suke tunani, kodai Annur ɗinsu ya warke daga haukan da yake yi ne? Mahaukaci ba zai taɓa yin irin wannan maganar ba, sai dai mai cikakken hankali. "Na tsince shi ne ya galabaita sosai, yana matuƙar jin ƙishi. Sai na fiddo da gorar ruwa daga motata na ba shi. A nan nake tambayarshi waye shi? Kuma ina zai je? Shi ne yake ce min shi ma bai san inda zai je ba. Bai ma san ta yadda akai ya baro gidansu ba. Na tambaye shi ko zai iya gane gidan nasu? Ya amsa min da ehh. Na samu da ƙyar motata ta tashi, ashe kan batir ne ya goce. A hankali muka taho yake gwada min, har muka iso nan." Kukan farin ciki Momy ta fasa da ƙarfi. "Annur ɗina hakan na nufin ka warke kenan?" Kanshi ya ɗaga alamar ehh. Sannan ya ƙara da faɗin, "Da gaske ne Amrah ta rasu?" "Amrarka ta rasu Annur. Ta rasu a daidai lokacin da ya rage satika kaɗan a ɗaura muku aure." Sai yanzu ya fahimci ko ita ɗin wacece a rayuwar Annur. Sai ya ce, "Ina matuƙar ƙaunar Amrah. Na so a ce ta ci gaba da rayuwa, mu gina rayuwarmu tare. Amma Allah bai nufa ba. Ashe dai mutuwa za ta mana yankan ƙauna, za ta raba jini da hanta." Cikin tausayawa Dady ya ce, "Ka yi tawakkali Annur. Ka ga irin haka ne fa ya sa ka samu matsalar ƙwalwa. Amma ga shi fitar da ka yi ɗin ma ta zame mana alkhairi baki ɗaya, tunda ga shi da alama ƙwalwarka ta zama normal. Ko ka faɗi ka bige kanka ne?" "Ni ma ban sani ba." Sans ya faɗa a hankali. * Washe gari da sassafe Bobby ya tafi ƙauyen Jani wurin boka, kamar yadda ya ma Sans alƙawari. Boka ya yi murmushi, ya ce, "Aikin kurciya na ɗaya daga cikin sauƙaƙƙun ayyukan da muke yi a nan. Saboda haka wannan ba wani babban aiki ba ne." Ya yi wani irin tsafi, sai ga kurciya mai kalar baƙi da fari ta ɓullo a gabanshi, idanuwanta jajaye, ta tsura su a fuskar boka Gagarabada, tana kallonshi ƙyam. *** Tunda ta kwanta take juyi. Sam! Barci ya gagara ɗaukarta. Tunanin rayuwa kawai take. Tunanin yadda komai ke faruwa tamkar a mafarki take yi. Wai aure za a mata a cikin ƴan kwanakin nan? Ita exam ɗin da za ta fara ma take ji, tana buƙatar samun nutsuwa sosai ta yi karatu, tunda second semester exams ce, wacce daga ita za ta shiga level 3. Wani tunani ne ya faɗo mata, hakan ya sa ta lalubo wayarta daga jikin chaji, ta latso kiran Jiddah. Ba ta yi tsammanin za ta ɗauka ba, lura da yadda dare ya tsala, ana neman ƙarfe ɗaya na dare ne fa yanzu. Sai da wayar ta kusa tsinkewa sannan Jiddah ta ɗauka, cikin magagin barci ta ce, "Maryam lafiya?" "Ba lafiya ba Jiddah." Maryama ta faɗa, a daidai sadda kuka ke zo mata. Tashi zaune ta yi Jiddah. Ta murje idanuwanta, haɗe da daidaita muryarta, ta ce "Me ya faru kike kuka Maryama? Ko jikin Yaa Noor ɗin ne ya tashi?" Maryama ta share hawayenta, wani na shirin sauko mata ta ce, "Ko kaɗan ba jikinsa ba ne ba, Jiddah." "To mene ne?" "Akwai abubuwan da suka faru ne..." Maryama ta kwashe komai ta sanar wa Jiddah. A ƙarshe ta ce, "Yanzu dai an tsaya a kan cewa za ki haɗa ni da kawun Annur, zan fayyace mishi komai, sannan a ƙarshe in haɗa shi da kawu Imrana, su yi magana. Wai ba za a saka Abba yin kaffara ba. Yadda ya rantse cewa aure zai min a cikin ɗan taƙin nan, to dole auren zai min, idan ba haka ba kuma zai haɗa ni da duk wanda yake so." Cike da tausayi Jiddah ta ce, "To ke Maryama me ya ja miki zaɓar mahaukaci a matsayin wanda za ki aura? Yanzu idan aka ɗaura muku auren, sai ya warke, ba kya tunanin zai guje ki? Ba kya ga kamar zai ce ba ya son ki? Maryama wallahi tsaf zai iya rabuwa da ke, tunda dai ba saninki ya yi ba. Bai kamata ki yanke wannan ɗanyen hukuncin ba. Ai da ki auri mahaukacin ma gwara ki auri Yah Deedah ɗin ma. Yanzu ina alƙawarin da kika ma Fiddou, kan cewa Annur zai koma gare ta ya aure ta?" Dafe kanta ta yi Maryama. Sosai take jin haushin kalaman Jiddah, daurewa kawai take. "Ba ma wannan ba, ni yanzu ina na wani san Kawun Annur? Ina ma na san yana da kawun ko bai da shi? Ni dai kawai na faɗa miki cewa Mamina ƙawar Momyn su Annur ɗin ce." "To ai a hakan za ki iya binciko mana komai Jiddah. Ke kaɗai ce za ki iya yi min wannan taimakon Jiddah, da ke kaɗai na dogara, you are my only hope, Jiddah. Ki rufa min asiri don Allah gobe mu haɗu, duk ma yadda za a yi a yi." Ajiyar zuciya Jiddah ta sauke. Sosai take jin tausayin ƙawar tata. Sai dai kuma gani take kamar zaɓin da ta yi bai kamata ba. Amma babu komai, za ta taimaka mata iya ƙarfinta, domin fitar da ita daga wannan ƙangin da ta faɗa. "Shi kenan Maryam. Allah ya kai mu goben. Insha Allahu da safe zan ma Mami maganar, cikin dabara zan binciki dangin mahafin nashi. Komai kenan zan kira ki na sanar miki." Da sauri Maryama ta ce, "A'a Jiddah. Kar ki ma Mami ƙarya. Ni yanzu na san illar yi ma iyaye ƙarya Jiddah. Ki faɗa mata gaskiya, wata ƙila ita ɗin ma akwai wani taimako da za ta iya yi mana." Jiddah ta ce, "To shi kenan. Insha Allahu zan faɗa mata gaskiya. Amma don Allah Maryam ki kwantar da hankalinki. Wannan kukan da kike yi ki daina shi. Dukkanin abin da ya yi tsanani to yana tare da sauƙi. Da yardar Allah komai ya kusa zuwa ƙarshe. Wannan damuwar da kike ciki dukkaninta za ta koma farin ciki." "To Allah Ya tabbatar mana da hakan Jiddah. Na gode ƙwarai, Allah saka miki da alkhairi. Sai da safe." "Ameen Maryam. Sai kin ji ni." Suka kashe wayoyin, kowacce da tunanin da take yi a cikin zuciyarta. Samun kanta ta yi da samun nutsuwa sosai a cikin zuciyarta. Bayan ta miyar da wayarta a jikin chaji ta miƙe, ta nufi ban-ɗaki domin gabatar da alwalla, ta yi ƙiyamul-laili, ta sanar wa Allah damuwarta, da neman agaji a wurinSa. * Washe gari da sassafe Maryama ta tashi. Sosai take jin dukkanin nutsuwarta da ta rasa tana dawo mata. Sassauci take ji sosai a cikin zuciyarta. Sauka ta yi daga bisa gadonta. Ta cire hijabin da ke jikinta, sannan ta nufi hanyar barin ɗakin, ta doshi kitchen. Dankalin turawa ta hau ferewa. Bayan ta gama ta kama aikin suyarshi, ta jajjaga tarugu da albasa da maggi, sannan ta fasa ƙwai ta ma Abbanta sauce ɗin ƙwai. Sai da ta gama duka sannan Mama ta shigo Kitchen ɗin. A tsammanin Maryama Mama ba za ta kula ta ba. Sai dai kuma ta ga akasin hakan. Da murmushi Mama ta ce da ita, "Sannu da ƙoƙari. Yau barci ya so ya ƙwace min wallahi. Allah dai ya sa kin tashi Hammad daga barci." Dafe kanta ta yi Maryama. "Shaf na manta Mama. Bara na hanzarta to. Har bakwai ta wuce." Da saurinta ta nufi ɗakin Mama, inda Muhammad ke kwana shi kaɗai. A zaune ta same shi. Ya ɗora tafin hannunsa na dama a bisa haɓarshi, ya yi zurfi a tunani.  Tsaye ta yi tana ƙare masa kallo. Ta rasa abin da yake tunani. Ba ta farga ba ta ga ya kuma juyawa, ya koma ya yi kwanciyar rigingine a bisa gadon ya ƙura ma wuri ɗaya kallo, hannayensa ya tallabe ƙeyarshi da su.  Take Maryama ta ji hankalinta ya tashi. Jiki saɓule ta iso gare shi. Ta saka hannunta na dama tana bubbuga shi. "Tunanin me kake haka Hammad?" Ta nemi wuri ta zauna. Sai a sannan ya ji ƙwalla ya zubo masa. Cikin muryar kuka ya ce, "Yaya Maryama ina tunanin rabuwa da ke ne. Wai yanzu shi kenan aure za ki yi ki bar ni? Tafiya za ki yi ki bar ni Yaya? Zan yi kewar ki sosai." Hawaye ya gama wanke mishi fuska. Hannunshi na dama ta kama ta riƙe. Cikin kwantar masa da hankali ta ce, "Ba na son ganin hawayenka ƙanina. Ka share su please. Don an ce za a min aure ai hakan ba wai yana nufin na bar ka ba kenan. Sannan kuma yanzu ko an yi auren ma ai a nan gidan za mu ci gaba da zama, har sai sadda Annur ya samu lafiya. So, ka kwantar da hankalinka. Okay?" Kai ya ɗaga mata kawai, ba tare da ya furta komai ba. "Then, stand up and act like a man, not a boy. Its already time for school. Hurry up and get ready for going to school." Cike da jarumta ya miƙe, ya nufi ban-ɗaki domin shirin makaranta. Gyaɗa kanta ta yi Maryama, tana jin tausayi haɗe da soyayyar ƙaninta na daɗa shiga duk wata kusurwa da take cikin zuciyarta. Bayan fitar ta ta samu babu kowa a falon, ta leƙa kitchen babu Mama, hakan ya sa ta nufar ɗakin Abba, tana jin zuciyarta na bugawa sosai, tunanin abin da za ta tarar daga wurin Abbanta. Zai kula ta ko ba zai kula ta ba?. "Mama na duba ban gan ki ba." Ta faɗa bayan ta duƙa har ƙasa, ta ce, "Barka da tashi Abba." "Yauwa." Ya faɗa ƙasa-ƙasa. "Ina kwana?" "Lafiya." Duk da yanayin yadda ya amsa mata gaisuwar, hakan bai hana ta samun sassauci a zuciyarta ba. Sosai ta ji daɗi, ta kuma tabbatar cewa ya rage jin haushinta, da alama Kawu Imrana ya roƙa mata gafara a wurin shi. "Kin tashi Hammad ɗin dai ko?" "Ehh Mama. Na tashe shi. Ya shiga wanka ma na baro ɗakin" Ta ƙarisa da fita ta bar ɗakin. Kai tsaye daga nan ɗakin Annur ta nufa. Fuskarta cike da fara'a. Zuciyarta na tsananta ƙaunarshi. Duk wata gaɓa ta jikinta tana jin yadda jijiyoyi da jininsu ke yawo da soyayyar Annur. *** *How y'all? I hope you're all fine. Ban ma san me zan faɗa ba. Bakina ya gagara furta komai. Zuciyata na cike da ƙaunarku. Hannuwana na cike da son rubuta sunan nan. RAZ NOVELLA 1. Ina yin ku, ina ƙaunarku, ina muku soyayya ta fisabilillah. Haƙiƙa na matuƙar jin daɗin comments ɗinku na jiya. Na yi farin ciki fiye da tunaninku. Ina fatar ɗorewar hakan, ba wai a kaina kaɗai ba, ga kowa ma.* *Masu mutunci ba sai na ce komai ba. Kun san me ya dace, I know.* Team Marnoor Team ANS Team Princess Amrah Team NWA Thanks all. Pinky durling💞 RAZ 2 [9/10, 7:30 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taɓa zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 6⃣0⃣ Wattpad: PrincessAmrah *** Runtse idanuwansa ya yi boka Gagarabadau. A hankali ya buɗe su, ya sauke a saman kurciyar. Take nashi idanuwan ma suka rikiɗe, sukai jajur, tamkar jan gaushi. Kallonshi take yi sosai kurciyar, a hankali idanuwanta na komawa normal, kamar na kowacce irin kurciya.  Haɗe dukkanin tafukan hannayenshi ya yi, ya kanga su a saman fuskarshi, ya rinƙa ambaton wasu irin kalamai, wanda shi kaɗai ya bar ma kanshi saninsu. Sai dai kawai yana ambatar Salman Sans, a cikin yaren nashi, sannan kuma sunan Annur ya biyo baya. A hankali kurciyar ta rinƙa tasowa sama, har ta iso a daidai saitin fuskar bokan, sannan ta dakata a saman iska. Ciro hannuwan nashi daga jikin fuskarsa ya yi. Sai ga wata irin ƙatuwar laya ta fito, ya saƙalo zarenta a jikin wuyan kurciyar, sanann ya sake yi mata wani tsafi. Jinin da ke cikin ƙwaryarsa ya ringa ɗiba yana watsa mata, a hankali ta rinƙa yin sama, har ta ɓula rufin ɗakin ta fice, sanann ya daina watsa mata ruwan. Murmushi ya saki mai ƙarfin gaske. Ya ce, "Ta tafi kenan, har abada. Ka ga yadda ta tashi sama, haka za ta ci gaba da tafiya, ba za ta tsaya ba har sai ta fice daga ƙasar nan, koma dai ina ne. To a duk inda ta dakata, a nan wanann mahaukacin zai dakata shi ma. Kamar yadda za ta ci gaba da rayuwa a wurin, shi ma a haka zai ci gaba da rayuwa a wurin. Duk ranar da ta tafi, shi ɗin ma zai tafi. Abu guda ɗaya ne tal zai iya dawo da shi garin nan. Shi ne a samu wani wanda zai cire layar nan daga wuyan waccan kurciyar, to lallai daga sannan zai iya dawowa garin nan, koma ta wacce hanya ce." Ajiyar zuciya ya sauke Bobby. Yana mai fahimtar dukkanin bayanan bokan. Akwai dokoki sosai na wannan aikin. Sai dai kuma ba wasu masu tsauri ba ne. Doka ta farko, babu soyayyar gaskiya (True love). Daga sadda ya aikata haka, lallai za a iya samun matsala da wannan aikin, komai zai iya lalacewa. Abu na biyu, zai samu karuwa, ina nufin mace mai zaman kanta, wacce zai rinƙa aikata zina da ita, na tsawon lokuta. Ina mai tabbatar maka da cewa, matuƙar ya tsaida dokokin nan, ya aikata komai yadda ya kamata, to zai dauwama a gidan. Rayuwarsa da komai za su koma ƙarƙashin mutanen, ba tare da kowa ya fahimta ba. Fatar kana fahimta." Kanshi ya ɗaga da sauri Bobby, ya ce, "Na fahimci komai Boka Gagarabadau." "Da kyau. Sai ka ɗauki ƙwaryar nan ka sha jini a madadin abokin naka. Ka ajje abin da za ka aje." Bayan ya ɗauki ƙwaryar ya kwankwaɗi jini, ya zaro kuɗi daga aljihunshi, ya ajje a gaban bokan. Sai da ya masa kirari sosai, sannan ya tashi ya tafi. Annur da ke zaune ya takure jikinshi, ya ɗora tafukan hannayenshi a bisa fuskar, yana sanye da wata baƙar T-shirt wadda Sans ya umurci Yax ya saka mishi.  Ji ya yi kamar wani abu ya daki zuciyarsa da ƙarfi. Bai san sadda ya miƙe tsaye ba. Ya fara waige-waigen gaba da bayanshi. Bai ga kowa ba, hakan ya sa ya gaggauta barin ɗakin da sauri, ya isa falo. Yax da Esien a zaune suna fira, suna ganinshi suka mimmiƙe da mamaki, Yax na faɗin, "Me ka fito yi?" Bai ko damu da su ba bare su sa ran zai amsa musu tambayarsu. Da iya ƙarfinsa ya bangaje Esien da ya matso daf da shi. Ya gaggauta isa bakin ƙofar, ya buɗe ta. Haka ya rinƙa tafiya da sauri da sauri, babu waiwaye haka kuma bai damu da kallon gabanshi ba, har ya fita titi. Tafiya ya yi sosai, sai dai idan ya gaji ya nemi wuri ya zauna ya huta, har duhu ya fara yi. A lokacin ya isa wani ƙauye ne, a bakin wata bishiya ya zauna hutun, bai ankara ba barci ya ɗauke shi. Shi ne bai farka ba sai da safe, kamar wanda ake tsikara ya miƙe, bai damu da yaran da suka zuba mishi ido suna kallo ba, ya ci gaba da zura sauri, har ya fice daga ƙauyen. Da haka da haka har Annur ya isa Maraɗi, inda ya ɗauki kusan kwanaki huɗu yana tafiya a hanya, kafin ya isa Maraɗin. Saboda dama daga Katsina zuwa Maraɗi ba wata tafiya mai tsayi ba ce. Sadda ya isa boarder, ƴan sandansu na can sun so su dakatar da shi, amma wani daga cikinsu ya ce su bar shi, tunda dai ba shi da hankali. Wannan dalilin ne ya sa rayuwar Annur ta koma Maraɗi. A ranar da ya isa ya haɗu da Fiddou, wacce ta taimake shi, ta ba shi dukkanin gata, tamkar dama can ta san shi. * Tun bayan da boka ya gama aiki, iyayen Annur suka samu kansu da samun nutsuwa sosai, dangane da Sans. Ko kaɗan babu wanda ya taɓa tunanin cewa ba Annur ɗinsu ba ne, duk kuwa da cewa ba duka abu ba ne za a ce iri ɗaya da Annur ɗin, dole za a samu bambanci komai ƙanƙantarsa. Sai dai kuma asiri ne ya ci su, ya ci dukkanin wani makusancinsu. Abokanan Annur baki ɗaya wanda suka zo yi mishi jaje, Sans ya wulaƙanta su, ya ci mutuncinsu, sannan kuma ya musu korar kare. Muguwar rayuwarshi ta shaye-shaye da bin mata ta ta'azzara. Baki ɗaya zuciyarsa ta gama ƙeƙashewa, ta bushe, babu tsoron Allah ko kaɗan a cikinta. A lokacin ne kuma Bobby ya gabatar da Annur a gidansu, cewa ga babban abokinshi, sun haɗu ne ta dalilin wani biki da suka yi. A take iyayenshi suka aminta da Sans, saboda asali sun san Pharm. IA. Sun san cewa mutumin kirki ne. Haka kuma yaransa na da tarbiyya sosai. Akai-akai ya rinƙa ziyartar likita, domin tabbatuwar lafiyar ƙafarsa, kuma ya yi nasara, ƙafar ta gyaru sosai, sai dai ƴan lokuta da ciwon yake ɗan taso mishi. Maganar aikinsa kuwa dole ya bar shi, saboda shi kam bai iya zane ba. Ko sadda suka koma wurin boka, sai dai bokan ya ce ya haƙura da zanen kawai, ya rungumi kowanne irin matsayi aka ba shi a kamfanin. Wannan dalilin ne ya sa ya bar zane. Ya zama CEO na kamfanin ƙere-ƙeren ƙarafan Pharm IA, aka nemi wani mai zanen daban. * Bayan wasu lokuta. Wasu mutane ne zaune a majalissa, sai fira suke a tsakaninsu, suna maida yadda akai. Kamar wasa suka ga wata kurciya ta faɗo ƙasa a inda suke, da laya maƙale a wuyanta. Wani daga cikinsu ya ce, "Ilu ji ikon Allah. Kurciya ce ga ta nan maƙale da laya a wuyanta." Wanda aka kira da Ilu ya ce, "Hala ma wani ne akai ma tsahi, aka korai daga garinsu. Wayyo Allah! Ke duniya, ina za ki tahi da mu?" Wani dattijo da ke zaune gefe ya ce, "Aikam cire ta nikai yanzu, babu ko ɓata lokaci." "Mallam Rabe mi ruwanka halan? Kai dai ka ƙyale ta, bari ma in tada ta ta tashi, koma ina za ta tai ta tahi." Mallam Rabe ya ce, "Kar ka kore ta Ilu. Cire layar nan daga wuyar kurciya ga ta, tamkar jihadi ne, mai matuƙar girma. Allah kaɗai ya san ladar da za mu samu, idan har wanda akai ma ita ya koma ga dangi nai." Kai suka jinjina su duka, alamun sun gamsu da zancen Mallam Rabe. Da sanɗo da dabara ya lallaɓa ya cafke kurciyar, tana ta ƙoƙarin zille mishi, amma ya riƙe ta tam! Bai sake ta ba, har sai da ya cire layar daga wuyanta. Jifa ya yi da ita, ba ta isa ƙasa ba ta tashi sama. Kwance layar ya yi, sai ga wasu irin tsummuna a cikinta, da takardu ƙanana-ƙanana, wani irin rubutu ƙunshe a jikinsu. Ƙwala ma wani yaro da ya zo gittawa kira ya yi. Bayan yaron ya zo ya ce, "Shiga gidan can ka ce in ji Mallam Rabe wai a bada ashana. Ka hanzarta ka ji." Da gudun yaron ya isa gidan, babu jimawa sai ga shi ya dawo, ya miƙa ta ga Mallam Rabe. Ƙyasata ta ya yi a layar, take ta kama da wuta. "Mutane babu imani. Ku kalli ku ga wannan mugunta don Allah. Yanzu ƙila wanda aka ma wannan kurciyar ya yi shekara da shekaru rabonshi da gidansu. To yau Allah ya yi, ƙarshen munahukan ya zo. Insha Allahu zai koma ga danginshi. Yau yau ɗin nan." Da haka zaman majalisar nasu ya kasance, cike da al'ajabin wannan al'amari. Daidai lokacin da suka cire layar kurciyar ne Maryama ta iso, suka tafi da Annur, zuwa ƙasarshi Najeriya, garinshi Katsina. *** Zaune yake a takure, hannunsa bisa haɓa yana tunanin duniya. Sosai ya yi zurfi a tunani, har ma bai san abubuwan da suke faruwa ba. Bubbuga shi ya ji an yi, ya zabura haɗe da shafe guntuwar ƙwallar da ta fito daga ƙwayar idonsa. "Annur..." Muryar Dadyn Bobby ce ta daki kunnuwanshi. "Na'am Dady." Ya faɗa cikin sassanyar muryarshi, wacce tun daga ranar da Farouk Sardauna ya rasu, ta koma haka. Komai nashi ya koma a nutse, tafiya ma kanta idan yana yi tamkar ƙwai ya fashe mishi a cikin cikinsa haka yake yin ta. "So nake in tambaye ka." Ɗora idanuwanshi ya yi a saitin fuskar Dadyn Bobby, tare da miyar mishi da dukkanin hankalinsa, don jin tambayar da za ta fito daga bakinsa ɗin. Sai da Dadyn Bobby ya sauke ajiyar zuciya, sannan ya ce, "Iya abubuwan da Farouk ya mallaka nake so na sani, idan kana da masaniya a kan wasu." Shiru ya yi Sans yana nazari, kafin daga baya ya ce, "Ehh to, na dai san akwai keke napep guda biyu da ake mishi haya da su. Sannan kuma ya zuba hannun jarinshi a Zamani Photography. Yana da Shop amma ba ta da girma sosai, ina ji ai kun san da wannan ma." Dadyn Bobby ya share guntuwar ƙwallar da ke ƙoƙarin fito mishi, don kar Sans ya gane. Ya ce, "Ehh tabbas na san da wannan. So nake duk wani abu da ya mallaka a siyarshi, sadaƙattul-jariyah nake so a mishi, ladar ta ci gaba da isar mishi har a kushewarshi. Tunda dai daga ni har Mamin tashi ba mu da gadonshi." Kuka ya kufce ma Dadyn Bobby, ba tare da ya so hakan ba. Duk da mamakin da Sans ke yawaita yi a duk sadda zai ji Dadyn ya yi makamanciyar maganar nan, hakan bai sa shi yin tambaya ba. Kewar abokinshi kawai ta ishe shi. "Su keke napep da wurin mai photography ɗin, duka zan bar komai a hannunka. Sai ka san yadda za a yi kuɗin su fito. Ni kuma zan je wurin mai shop ɗin, zan ƙoƙarta siyen duk abubuwan da suke cikinta. Idan an tattara kuɗin duka, za a gina masallaci koda ba mai girma sosai ba. A zuba carpets da butoci, sannan zan ƙara da kuɗina a gina rijiya. Allah ya jaddada rahama ga Umar Farouk." Ya gaggauta miƙewa ya bar wurin, gudun kar kukan nasa ya yi ƙarfi sosai, hankalin mutanen da ke wurin ya karkata gare shi. Shi kanshi Sans kukan yake iya ƙarfinsa. Wannan rashin shi ne na huɗu da aka masa a rayuwarsa. Abbunshi, Aunty, ƙanwarshi Yamairah, sai kuma ga babban abokinshi, mutumin da ya kyautata mishi, ya ba shi dukkanin abin da yai rashi a baya. Ya ba shi farin ciki tamkar dama can ya san shi. Shi ma ya tafi ya bar shi. Tafiya ta har abada. Kuka ya kuma fasawa, haɗe da haɗa kanshi da guiwa, yana shessheƙa. Wani bawan Allah cikin ƴan zaman gaisuwar ne ya matso inda Sans ɗin yake, ya ce, "Yaro ina kula da kai, tun daga ranar da Farouk ya rasu kodayaushe cikin kuka da damuwa kake. Wa ya faɗa maka kukanka zai taɓa dawowa da shi duniya? Ko ka manta cewa manzon Allah SAW ma ya yi wafati? Saboda haka dole kowa ma zai tafi. Allah maɗaukakin sarki ya ce dukkan mai rai mamaci ne. Don haka shi ma Farouk ba gaggawar tafiya ya yi ba, lokacinsa ne ya yi. Ka daina wannan kukan, ka fitar da duk wata damuwa daga cikin zuciyarka. Ka saka a ranka cewa tafiyar Farouk lokacinsa ne ya yi, duk daren daɗewa kai ma za ka bi shi. Kar ka ma ja ma kanka wannan damuwar ta jaza maka wani ciwon." Kansa ya ɗaga Sans, ya shanye kukansa, yana faɗin, "Na gode ƙwarai baba." *** Zaune take a bisa sofa, tana son ta kira Jiddah sai dai kuma ba ta so ta takura mata, tunda ba haka suka yi da ita ba. Jin ƙarar wayarta ne ya sa ta sauke ajiyar zuciya, sannan ta duba mai kiran. Sunan Jiddah ta gani ɓaro-ɓaro, hakan ya sa ta jin farin ciki ya lulluɓe zuciyarta. Tana fatan jin alkhairi a tattare da Jiddah. Har wayar ta tsinke ma ba ta sani ba. Farin ciki kawai take. Kafin Jiddah ta sake kiranta ita ta kira. Bugu ɗaya Jiddah ta ɗauka. "Amarya kin sha ƙamshi." Kawai ta jiyo Jiddah ta faɗa, tana faɗaɗa dariyarta. "Bana son iskanci fa Jiddah. Ai ke ce amaryar." "Malama kar ki kawo min raini. Na tabbata kina nan kina jin daɗin sunan da na kira ki da shi." Maryama ta murmusa, ta ce, "Ashe ma jin daɗi. Ni dai ba wannan ba. Ki faɗa min abin da nake son ji daga gare ki." "Hmm! Kuma har ki wani ce bakya so don na kira ki amarya? Na tabbata kin ji daɗi sosai." "Jiddah." Maryama ta faɗa. Sosai Jiddah ta gano nufin Maryama. Ba ta cika son tsawaita abu ba. Komai ta fi son jin shi direct. "Mun yi magana da Mama. Na mata bayanin komai dallah-dallah, tun daga farko har ƙarshe. Kuma Alhamdulillah! Ta fahimci komai, ta kuma tausaya miki. So, a yanzu dai ta ba ni lambar wani Class mate ɗinsu, wanda yake ƙanin mahaifin Annur ne. Sunanshi Uncle Marwan. Ta tabbatar min cewa yana da kirki sosai, kuma zai fahimce mu. Ta ma ce min za ta kira ta mishi bayanin za mu zo mu same shi, sannan mu ɗin ma mu sake kiranshi. Idan mun je kar mu ɓoye masa komai, tun daga farko har ƙarshe mu sanar masa, da izinin Allah zai ba mu dukkanin taimako, zai kuma goyi bayanmu ɗari bisa ɗari." Kamar ta yi ihun murna haka ta ji Maryama. "I don't even know what to say. Na matuƙar jin daɗin wannan zance. Yanzu ya kenan?" "Zan kira shi yanzu, mu ji inda yake. Sai ki gaggauta shiryawa, saboda ko Office ta kama mu same shi sai mu same shi ɗin. Mami ta ce min wai a State Inland Revenue yake aiki." "To shi kenan Jiddah. Kin yi ƙoƙari sosai wallahi. Allah kaɗai ya san ladar da zai ba ki. Bari in je in sanar da Mama, sannan in hau shiri. Ina ji akwai mota ma ajje, da ita kawai zan zo." Jiddah ta ce, "To shi kenan. Sai kin zo ɗin." Suka katse wayoyin. Tsalle ta buga Maryama bayan ta haye bisa gado. Ba komai ya mata daɗi ba illa jin da ta yi cewa mutumin kirki ne Kawu Marwan ɗin, kuma lallai zai fahimce su. Fita ta yi zuwa falo. Mama ba ta ciki, hakan ya sa ta nufi ɗakinta. A nan ta same ta tana duba wata takardar addua. Bayan ta yi sallama ta zauna a ƙasa, har sai da Mama ta gama ta ninke takardar adduar, ta miyar a cikin side drawer. "Miss complain. Akwai magana a bakinki, na ga alama. Mene kuma?" Bayan Maryama ta sunkuyar da kanta ƙasa. Ta ce, "Mama yanzu muka gama waya da Jiddah. Ta ce min wai sun yi magana da Maminsu, har ma ta ba ta lambar wani kawun Annur. To dai wai za mu same shi, mu mishi bayanin komai. Yanzu." Ajiyar zuciya ta sauke Mama. Ta ce, "To shi kenan. Don Allah a kula sosai Maryam. Allah ya taimaka ya sa abun ya zo da sauki." "Ameen Mama. Zan je in shirya." Ta miƙe tsaye, ta fara taku har zuwa ɗakinta. Cikin lokacin da bai wuce minti talatin ba ta gama shirinta tsaf. Jallabiya ce ta saka baƙa, mai adon silver. Ba wata kwalliya ta yi ba, powder kawai ta shafa da lip gloss, sannan ta ɗauki silver hand bag ɗinta, ta ɗauki wayarta ta fito. Sadda ta fito Mama na falo. Sallama ta mata, ta umurce ta da ta shiga ɗaki ta ɗauki dubu ɗaya ta ƙara mai a mota, sannan ta ɗauki mukullin mota, ta mata fatar alkhairi ta tafi. Kai tsaye gidan su Jiddah ta nufa. Ta same ta ita ɗin ma ta shirya, kamar haɗin baki ta saka baƙar jallabiya, amma ita baƙi ne zalla har adonta. Gaisawa ta yi da Mamin Jiddah. Bayan nan ta musu kyakkyawar addua, sannan suka tafi. Dayake ya ce musu bai je Office ba yana gida, address ɗin shi da ya turo ma Jiddah ta text message suka bi, babu wahala sai ga su a cikin GRA, road K. House No. 16 ne gidan nashi, hakan ya sa suka dakata a nan, haɗe da yin horn. Babu ɓata lokaci mai gadi ya wage musu gate, kamar yadda kawu Marwan ɗin ya ce da Jiddah, idan sun iso kawai su zarto har cikin gidan. Parking space suka dosa, motoci ne manya-manya a girke, wanda za su kai kimanin guda biyar, sai wani babban bike daga gefe. Junansu suka kalla a lokacin da suka fito daga motar, ba su san inda za su dosa ba, saboda girman gidan. Jiddah ce ta koma wurin mai gadi ta tambaye shi ta inda za su bi su shiga gidan. Ya gwada musu ƙofar gaba, wadda za su fara cin karo da babban falon mai gidan. Sai kuma ya musu kwatancen ƙofar baya, ita kuma ita ce za ta sada su da ainahin inda iyalin gidan suke. Sai su zaɓi ta inda za su bi. Maryama ce ta ce mafi a'ala dai su fara shiga inda iyalinshi, su gaisa sannan a musu iso zuwa ga kawu Marwan ɗin. Abin da suka yi kenan. Sun ci karo da babban tsakar gida, inda masu aiki ne jere rinkis, kowa na aikin gabanta. Bayan sun yi sallama Jiddah ta ce, "Don Allah ina masu gidan?" Wani ɗaki ɗaya daga cikin masu aikin ta gwada musu. Nan ɗin suka nufa kuwa, sai ga su a wani hamshaƙin falo, wanda ya ni'imtu sosai da kayan more rayuwa. Bene ne daga can gefenshi, da alama ta nan ake bi idan za a shiga bedroom.  Babu kowa a falon, sai suka rasa ma yadda za su yi. Tunani suke, kar ma a je mai gidan ta wulaƙanta su. Saboda wannan tarin ni'ima da take cikinta, ba kowacce mace ce za ta iya tarbar mutane yadda ya kamata ba. Zama suka yi bisa 2 seater, suna zaman jiran tsammani. Wata yarinya ce suka ga ta sauko daga bisa benen, ƴar kimanin shekara biyu. Sanye take da ƴar kanti pink, gashinta an gyara shi da ƙananan ribbons su ma pink. Har rige rigen tambayarta inda mamanta take suke, up stairs kawai ta gwada musu da hannu. "Ki kira ta kin ji. Ki ce wai baƙi ne suka zo." "She's sleeping." Yarinyar ta faɗa, cikin gwarancin rashin iya magana. Jiddah ta taɓe baki. Haushi ma yarinyar ta ba ta. Da alama irin yaran nan ne da ake ɓatawa da kilbibi ba a musu Hausa. "Ok. Where's your father?" Maryama ta mata wannan tambayar. Kwakkwaɓe baki ta yi yarinyar kamar za ta yi kuka. Ita a dole sun dame ta da tambaya. Tafiyarta ta yi zuwa sama, ba tare da ta sake ce musu komai ba. Tsoki suka saki a tare. Jiddah ta ce, "Maryam tashi mu nufi part ɗin mai gidan, tunda dai ya san da zuwanmu." Suka miƙe, haɗe da ficewa daga part ɗin ma baki ɗaya. Ta ƙofar gaba da mai gadin ya fara gwada musu suka nufa. Sai da suka yi knocking ya ba su izinin shiga, sannan suka cire takalmansu, suka nufi cikin falon. Ai ƙawatuwar da ɗakin ya yi, har ma ta zarce na part ɗin matarshi. Kishingiɗe yake bisa tafkeken kafet ɗin ɗakin. Ya tsura idanuwansa a tv yana kallon news a Liberty TV. Cike da annuri ya amsa sallanar tasu, yana faɗin "Ku ƙariso daga ciki mana." Ɗar-ɗar kawai suke su duka biyun. Ba su yi mamakin karamcin mutumin ba, saboda dama Mamin Jiddah ta faɗa musu, cewa yana da kirki sosai, tamkar ba mai kuɗi ba. Har ƙasa suka duƙa suka gaishe shi, sannan ya ce da su su tashi su hau bisa kujera. "Ayyub!" Ya ƙwala ma wani kira. Take wani matashi ya bayyana, sanye da irin kayan kuku, har da hularshi. "A yi serving ɗin su." Da sauri Jiddah ta ce, "Wallahi Baba dama an bar shi. Daga gida muke kai tsaye." "A'a 'ya'yana, kar mu yi haka da ku. Ayyub kawo musu ko drink ne." Da saurinshi ya bar wurin, bai jima ba sai ga shi ya turo wani keke, lemuka kala-kala jere a bisanshi, da kuma wasu irin haɗaɗɗun cups a kai. A gabansu ya hau jerawa, yana gamawa ya tafi ya bar su. Kaɗan suka sha drink ɗin, sannan Uncle Marwan ya ba su damar bayani. Tun daga kan zancen Amrah Maryama ta ɗauko mishi, ya san zancen sosai, saboda har ce mata ya yi ma shi ya nemo auren Amrah ɗin ma. Daga nan ta ci gaba da yi mishi bayani tiryan-tiryan, na yadda duk abubuwan suka wakana, iya wanda ta sani. A inda ta dakata, na auren dolen da ake so a mata, sai Jiddah ta ci gaba da ba shi labarin. Sosai mutumin ya yi mamaki. Ba don daga bakin Hajiya Safiyya ya fara jin zancen ba, kuma ita ta ce mishi yaran za su zo, to da tabbas zai ƙaryata su ne. Saboda shi dai a iya saninshi, Annur ba ƴan biyu ba ne. To ta yaya za a samu mutum mai irin kamanninshi sak! Babu bambanci? Ya yi zurfi sosai a tunani. Kuma sai wasu abubuwa suka fara faɗo mishi a rai, wanda suka fara gasgata mishi zancen na su Maryama. Tun daga sadda aka ce Annur ɗin ya warke, baki ɗaya ya rikiɗe daga mutumin kirki izuwa mutumin banza. Halayenshi kaf suka canza, daga na arziƙi zuwa na tsiya. Dafe kansa ya yi, ya sauke nannauyar ajiyar zuciya. "Akwai rikitarwa sosai a wannan lamarin. To amma me ya hana ku miyar da shi gaban iyayenshi, kuma ku musu bayanin komai?" Maryama ta ce, "Kawu akwai damuwa ne. Babu wanda ya san manufar wancan mutumin banzan. Allah kaɗai ya san abin da ya ƙulla, kuma yake da niyyar ƙullawa a duk sadda ya ga Annur ya koma gida. Na so a ce ya samu sauƙi sosai, kafin mu miyar da shi gida. Akwai wani likitan ƙwaƙwalwa da aka haɗa ni da shi, to duk tashin hankalin nan ne ya dakatar da abun, tunda a Maiduguri yake likitan." Shiru ya ɗan yi Uncle Marwan, kafin ya ce, "Kuma ke ma kin yi tunani mai kyau. Yanzu yadda za a yi, ki ba ni lambar kawun naki. Insha Allahu za mu yi magana da shi, yau-yau ɗin nan ma ba gobe ba. Ni zan zama wakilin Annur, za a ɗaura muku aure a cikin kwanakin da Abbanki ya bayar." Ya yi shiru, sannan ya ce, "Kuma ma kun san wani abun mamaki? Tun daga sadda na auro matar nan tawa, lokacin ƙila shi wancan mugun ba zai wuce ƴan watanni da zuwa gidan ba. Nake ta bin kanshi ya zo su gaisa amma ba ya zuwa. Wancan Annur ɗin ɗana kuwa, kafin matata ta rasu kusan kodayaushe yana gidan nan. Koda ba ya ƙasar da damar ya zo to sai ya zo inda take sun gaisa. Amma ita wannan bai taɓa zuwa ba ya gaisa da ita ba. Kuma shi ba ma'abocin zama gida ba bare idan na kai ta su gaisa. Tun ina magana ma har na gaji na daina." Jinjina kansu suka yi su duka biyun, kawunansu sunkuye a ƙasa. "Ku saka a ranku cewa auren nan tamkar an yi shi ne. Da izinin Allah." Da murna Maryama ta haɗa ido da shi. Zuciyarta na daɗa hauhawa da dukkanin farin ciki. Damuwarta na wucewa, tana jin yadda zaɓin Deedah da aka mata ya rikiɗe ya zame mata alkhairi. Ko ba komai idan ta zama mallakin Annur, ta zama halaliyarsa, za ta fi tsayawa ta kula da shi yadda ya kamata. Za ta ba shi dukkanin lokacinta. Za ta kula da shi, za ta tsabtatar da shi, sannan ta gwada masa irin soyayyar da mata ke gwada wa mijinta. Kasantuwarshi mahaukaci ko kaɗan ba zai sa ta ƙyamace shi ba. Duk wata kula da ta dace ta sha alwashin ba shi ita, har izuwa lokacin da zai samu lafiya. Sannan kuma ta ɗaukar wa kanta wani alƙawari, duk lokacin da Annur ya samu lafiya, ya nunar da ba ya son ta, to za ta haƙura da shi, za ta bar shi ya nemi zaɓinshi ya aura. Dama dai burinta ya samu hankali, komai nashi ya dawo daidai, kamar yadda ta yi alwashi. "Ku ba ni lambar kawun kawai, sai ku tashi ku tafi. Kar ku ji komai, na muku alƙawarin komai zai zo yadda ya kamata, kuma babu wanda zai ji komai daga bakina, ciki kuwa har da iyalina." Farin cikinsu bai iya ɓoyuwa ba su duka biyun, jaddada godiyarsu suka rinƙa yi, har suka ƙarisa miƙewa tsaye. Matsawa ya yi ga drowar tv stand, ya zaro kuɗi bandir na ƴan ɗari biyu, ya miƙa musu. Ƙin karɓa suka yi, suka masa godiya. "Kun ko san yadda na tsani na ma mutum kyauta ya ƙi karɓa? Ai ba roƙo na kuka yi ba ko. Manzon Allah SAW ya ce "La yaruddul khairu illasshaiɗan. (Babu mai miyar da alkhairi sai sheɗani.)" Saboda haka in dai ba so kuke mu ɓata ba, to ku karɓa." Jiddah ce ta duƙa har ƙasa cikin girmamawa ta karɓa, sannan suka mishi sallama, yana mai jan Maryama cewa sarakuwarshi, cike da kunya take sakin murmushi har suka fita. Bayan sun isa mota suka tayar, mai gadi ya buɗe musu gate. Suka tafi. Lambar Kawu Imrana ta gano, ta rubuta mishi text cewa sun gama magana da kawun Annur ɗin, har ma ya karɓi lambarshi, cewa yau ɗin nan zai kira shi, za su haɗu su yi magana. Gidan su Jiddah suka fara zuwa. A falo suka samu Mami tana waya. Zama suka yi har ta gama. "Da alama yaran nan nawa sun yi nasara. Saboda fara'ar da ke fuskarsu kawai ta isa ta tabbatar da hakan." Murmushi Jiddah ta yi. "Mami mutumin nan yana da kirki sosai. Ashe uwar gidanshi ta rasu." Mami ta ce, "Wallahi kuwa ta rasu Jiddah. Ai dalilin da ya sa ma nake da lambarshi kenan, sadda ta rasu dayake ba a ƙasar nan ta rasu ba, kansar jini ce ta kama ta, aka kai ta India. To dai na sa Hajiya Suhaila ta ba ni lambarshi, na kira na masa gaisuwa. Ai kusan yaransu ma duk manya ne. Suna America su ukun duka a can suke karatu. Ɗiyarshi ta biyu ai sa'ar yayarku Rabiatu ce. Ɗiyarshi ta biyu kuma sa'ar Zarah ce. Sai wanann shuwar da ya auro, ita kuma ɗiyarta ɗaya kacal, sunan ɗiyar tata Shereefa." Gyaɗa kawunansu kawai suka yi, sannan suka hau ba ta labarin duk yadda suka yi da shi. Sai kusan bayan la'asar sannan Maryama ta koma gida. Muhammad da Mama ta samu a falo suna hira. Muhammad na ganin ta ya ce, "Yaya Maryama tun ɗazu nake ta fama da Mama ta ara min wayarta in kira ki ta ƙi. Ta riƙe a hannunta don ma kar in ɗauka." "Allah sarki yarona. Ai ga ni na dawo. Mama mun je mun samu kawun na Annur, an gama komai. Har ma na haɗa shi da kawu Imrana." Da faraa Mama ta ce, "Kai masha Allahu! Lallai abu ya yi kyau." Maryama ta kalli Muhammad, "Hamnad Jiddah ta ce in gaishe ka wai." "To ina amsawa. Ɗazu da na kai ma Yaya Annur abinci yake tambayana kina ina?" Cike da mamaki Maryama ta zuba ma Hammad idanuwanta, ta ce, "Annur ɗin ne ya tambaye ka ina ina?" Kai ya ɗaga mata alamar ehh. Mama ta ce, "Ki tabbatar da ya sha maganinshi fa. Don Hammad na aika, ban tabbatar ba ko ya sha ko bai sha ba." Muhammad ya ce, "Allah kuwa ya sha Mama. Shi da kanshi ma ya gwada min yadda yake sha." Murmushi kawai Maryama ta yi sannan ta nufi ɗakin Annur ɗin. Zuciyarta sayau, sai farin ciki take yi. * "Alhaji Marwana ka dai ƙi shan ko ruwa ko?" "A yi haƙuri Alhaji Imrana. Bari in sha jan ruwa to." Murmushi suka yi su duka biyun, kafin Alhaji Marwana ya ce, "Kar ka ji komai Alhaji Imrana. Ina mai tabbatar maka da cewa komai zai daidaita. Na ɗauko ƙafafuwana ne musamman domin na nemi auren Maryama ga ɗana Annur." Ya karkace ya zaro kuɗi daga aljihunsa. Bandir ne na ƴan ɗari biyar, dubu hamsin kenan. Ya dire su a bisa teburin gabanshi, ya ce "Ga wannan Alhaji Imrana. Kuɗin neman aure ne. Sadda duk kuka tsaida ranar ɗaurin aure, zan zo da kuɗin sadaki, kafin nan kun fidda ko nawa ne." Kawu Imrana ya ce "Yau alhamis, gobe jumua, insha Allahu rana aita gobe za a ɗaura auren Annur da Maryama. Nan da kwanaki takwas kenan. A kan sadaki naira dubu hamsin." Da haka sukai sallama, har bakin mota kawu Imrana ya raka Alhaji Marwan, dukkaninsu suna jinjina mutunci da karamcin junansu. *** *My pipu, how y'all? Ya kuka ji wannan chapter ɗin? 5k words kenan na muku, har da ɗori ma. Ƴan RAZ NOVELLA 1 sai ku sakar min mara, yau dai kam kun samu yadda kuke so. Amma fa na sha aiki, sosai ba kadan ba. Wash!* *Finally, an saka ranar aure nan da kwana takwas. Masu fitar da ashobe, ku muke jira. Lol.* *Masu karatu me kuka hasko ga wannan matar ta Alhaji Marwana wadda aka ce ba ta taɓa haɗuwa da Sans ba? Ni dai kam na fara hango wani abu, amma bari na kame bakina har mu zo wurin sannan. Me kuke hasashe? Idan har aka samu mutum goma da suka canko daidai, lallai zan muku shafi guda gobe idan Allah ya kai mu, duk kuwa da cewa babu tsarin hakan a tattare da ni.* *Masu mutunci ko kun san cewa saboda ku na dage rubuto wannan zungureren shafin? Ina jin daɗin yadda kuke kankaro mutunci, shi ya sa nake ƙoƙarta kankaro muku mutuncin ni ma.* *Ƴan laɓe kuma ku ci gaba da yi, Allah na ganin ku.* Thanks all Pinky durling💞 RAZ 2 [9/11, 8:01 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 6⃣1⃣ Wattpad: PrincessAmrah *** Yana ganin ta ya miƙe tsaye, fuskarsa ƙunshe da faraa. Ita ɗin ma faraa ce a tata fuskar, ta ce, "Ya Noor..." Kafin ta ƙarisa faɗin abin da za ta faɗi, ta ji ya ce, "Maryama yau ba ki min bankwana ba kika fita. Sai da wannan ɗan yaron ya zo ya ce da ni kin fita." Kallonshi take sosai. Ba ƙaramin kyau ya mata ba. Pink ɗin riga ce a jikinshi mai dogon hannu. Kallo ɗaya idan mutum ya masa zai iya cewa mutum ne mai hankali. Saboda tufafin jikinsa, sabbi ne dal Maryamar ta siyo mishi. "To koma ka zauna. Akwai albishir na musamman da zan maka." Babu musu kuwa ya koma ya zauna ɗin. Yana bin ta da kallo. Zaman ta yi ita ma a gefenshi, ta ce, "Na je ne a kan maganar aurenmu ni da kai." Dariya ya yi bayyananna, ya wangale baki dukkanin haƙoransa suka bayyana, sannan kuma ya saka tafukan hannunshi ya kare fuskar tashi.  Murmushi ta sakar mishi Maryama. Ta ce, "Ka ma daina rufe fuskar nan Mallam. Gwara ka buɗe ta ka ba ni labarin me ka tanadar min a matsayin amaryarka?" Shiru ya yi har yanzu yana jin kunyarta. Gyaɗa kanta ta yi, a zuciyarta tana faɗin da alama dai dama can asali Annur mutum ne mai kunya. Saboda komai ƙanƙantar abu sai ya kama rufe fuskarshi, a dole ya ji kunya. Ɗan taunar leɓonta ta yi a hankali, ta runtse idanuwanta, tana buɗewa ta ɗauke su a kyakkyawar fuskar Annur, wadda ta ƙawatu da murmushi. "Mun je gidan Kawu Marwan ne." Ta faɗa, ba tare da ta ɗauke kallonta daga gare shi ba. "Kawu?" Ya ɗan yatsine fuska alamar tunani. "Uncle Marwan nake nufi." "Uncle Marwan?" Ya faɗa idanuwanshi a buɗe. "Ehh. Ka san shi ne?" A bisa haɓa ya ɗora hannunshi alamun tunani. Can kuma ya ce, "A duniyar su Amrah ne kawai na san wani Uncle Marwan." Jinjina kanta ta yi Maryama. "Da alama sauƙi na samuwa. Ga shi sannu a hankali idan an ambaci wasu sunayen kana tuna ka san su koma yaya ne." Ta faɗa a bayyane. "Barin tafi ɗakina. Wanka nake so in watsa. Anjima da dare insha Allahu zan dawo, kuma sai ka faɗa min tanadin da kake ma amaryarka." Tana fita ta tarar da ƙawar Mama ta zo, da babbar leda a gabanta. Har ƙasa ta duƙa ta gaisar da baƙuwar sannan ta miƙe za ta nufi ɗakinta. "Maryama." Mama ta kira ta. Hakan ya sa ta dawo, haɗe da durƙusawa a gaban Mama. "Na ma Hajiya Maria maganar ashobe ne. To shi ne ta zo da su wai a zaɓa, duk da dai ƙurewar lokaci. Amma dai ai ba a yi biki haka nan ba, kuma bikin farko a gida. Takwararki ce ma ta kira ni, cewa gaskiya dole a fito da ashobe, mai halin yi ta yi. To kun ga dai wanda na fitar nan, ban san ko sun yi ba." Laces ne guda biyu iri ɗaya, ɗaya baƙi sai ɗayan yellow, masu matuƙar kyau.  "Kin gan su nan. Duka biyun sai a bar su a matsayin ashoben ne. Kun ga duk mai raayin baƙin sai ta yi, mai raayin yin yellow kuma sai ta yi. Ya yi kyau ai ko?" Cike da kunya Maryama ta miƙe tsaye. "Da ke fa nake magana kika min shiru." Susar kanta ta hau yi Maryama. "Ni dai Mama duk wanda aka yi ɗaya ne. Wanda aka fitar zan ɗauki hoto in tura ma Jiddah." "To ai shi kenan. Sai ki tafi." Barin ɗakin ta yi tana mai tsananin jin kunya. Wanka ta yi Maryama, ta saka riga da skirt na English wears, kalar ash and pink, wanda suka matuƙar hawa jikinta. Abubuwa uku ne suka faɗo mata a rai lokaci guda. Na farko alƙawarin da ta ma Fiddou, kan cewa duk daren daɗewa za su koma gare ta, kuma Annur zai aure ta. Wani irin kishi ne ta ji ya turnuƙe zuciyarta. Ya za ta yi? Dole ta cika mata wannan alƙawarin, duk kuwa da yadda ba ta so ɗin. Abu na biyu da ya faɗo mata a rai shi ne, ƙarshen wayarta da Bobby. Haka kawai ta samu kanta da faɗuwar gaba. Baki ɗaya hankalinta ya tashi. Tausayinsa take, duk da dai cewa a ganinta babu ko kaɗan ɗin soyayyarsa a cikin zuciyarta. Dole za ta kira shi a waya, ta ji yaya jikin nashi a yanzu? Abu na uku kuwa Dr. Hamdan M. Ramat ne ya faɗo mata a rai. Missed calls ɗinsa da ta gani har guda biyu, wanda tashin hankali bai bar ta ta kira shi ba. To yanzu me za ta ce da shi idan ta kira shi ɗin? Dole dai ta daure ma kiranshi ɗin, ko ma ya za a yi a ƙarshe sai an yi. Lambar Bobby ta fara ganowa. Kamar kar ta latsa kiran nashi, wata zuciyar dai ke daɗa ingiza ta a kan ta daure dai ta kira shi ɗin. Bugawa take ta yi amma ba a ɗauka ba. Sai a kira na uku da ta yi ne Sans ya ji ringing ɗin wayar. Dubawa ya yi ya ga mai kiran, sai kuma maganar Bobby ta faɗo masa a rai. Inda yake ce masa duk sadda mutuwa ta ɗauke shi, to ya taimaka ya cika mishi burinshi, ya auri Maryama. Saboda tana da hankali sosai, kuma ya tabbata ba za ta ƙi shi ba, ko don wasiyyar da ya bar mata. Idonshi cike taf da ƙwalla Sans ya ɗauki wayar ya kanga a kunnenshi. Yanayin yadda ya ajje kalmar Hello kaɗai ya tabbatar mata da cewa ba Bobby ba ne wannan. Ta so ta gane muryar, duk da cewa ba da yawa sosai suka rinƙa yin waya da Sans ɗin ba, amma dai muryar ta mata kama da tashi. "Ahmm...! Don Allah Farouk Sardauna fa?" Sai da ya runtse idonsa sosai, yana son daurewa, amma ina, abun ya gagare shi. Dole sai da shessheƙar kukansa ta fito. Take hankalin Maryama ya tashi. Ido a buɗe ta ce, "Farouk ɗin ba ya kusa ne? Please ka ba shi. Ka ce da shi Maryama ce." A ruɗe take sosai. Wannan kalaman ma da ƙyar ta samu ta haɗo su. "Ki yi haƙuri, amma Farouk ya rasu yau kwana uku kenan. Kwananshi biyu a kushewarsa." Kamar saukar aradu haka ta ji kalaman. Farouk ya mutu? Ta sake maimaitawa a cikin zuciyarta. Ba ta san sadda kuka ya kufce mata ba. Cikin kukan take cewa, "Allah sarki Farouk! Ashe dai ciwon na mutuwa ne. Ashe tafiya za ka yi Farouk. Ashe ba ka zamanto daga cikin masu tsawoncin kwana ba..." Kuka sosai take yi. Tana tuno wasu abubuwan nashi. Yadda ya nuna mata ƙauna. Ya so ta, soyayya ta tsakani da Allah. Ya nemi shiryuwa duk don saboda ƙaunar da yake mata. Ashe da gaske wasiyya ce yake ba ta a sadda suke wayarsu ta ƙarshe? "Farouk me ya sa ka tafi? Wallahi da gaske ina ƙaunarka. Ina son ka har cikin zuciyata Farouk. Halayenka ne na ƙi, ba kai ba Farouk. Allah ya ji-ƙanka, ya haskaka makwancinka. Allah ya rahamshe ka. Allah ya gafarta maka dukkanin kura-kuranka." Kukan da ya ci ƙarfinta ne ya sa ta ajje wayar, ba tare da ta kashe ba. Yana jin yadda take kuka sosai. Yana jin yadda kalaman ke fita kai tsaye daga cikin zuciyarta. A take mutuwar abokinsa ta rinƙa dawo mishi sabuwa dal. Zafin rashin Farouk na daɗa ruruwa a cikin zuciyarsa. Ji yake ina ma dai a ce bai ɗauki kiran ba sadda ta kira? Da ya huta. Da ba ta tado mishi da tabon da har yanzu bai gama warkewa ba. Da ƙyar ya samu ya katse wayar. Kuka yake sosai, jikinsa sai rawa yake. Nadama yake, nadamar munanan halayensa. Me ya sa ba su zama mutanen kirki ba? Me ya sa ba su zama wasu mutane wanda za a yi alfahari da su ba? Gyaɗa kanshi yake, yana mai istighfari a gurin Allah. Rahamar mahaliccinsa yake nema wa abokinsa. So yake ya jure, ya ci gaba da neman gafarar Allah. Amma ina, damuwa ma ba za ta taɓa barinshi ba. Kuka da zullumi ba za su taɓa barin shi yin istighfarin ba. Wani irin zazzaɓi ya ji yana sauko mishi. Tun jiya yake jin alamunshi, yana son zuwa mishi. Sai dai bai samu damar saukar ga baki ɗaya ba sai yanzu. Abu biyu ne suka haɗe mishi, suka saka shi zazzaɓin. Na farko kukan da yake yawaita yi. Na biyu kuma kayan maye da ya kwana biyu bai sha ba, rashin shan su ne ya yi maƙasudin hakan. Drip kawai za a saka mishi ya samu sassauci. Miƙewa ya yi jiki babu kuzari, ya saka wayar Bobby a aljihunshi, dama saboda kiran da ake mishi ne ya sa Dadyn Bobby ɗin ya sa ya ajje wayar a wurinshi. Kai tsaye chemist ya nufa, domin samun taimakon gaggawa. Maryama kuwa kuka ta shara sosai, tamkar wacce aka ce ta yi rashin iyaye. Tausayinsa take ji. Sai yanzu take jin tsantsagwaron ƙaunar Farouk Sardauna na shiga duk wata kusurwa ta cikin zuciyarta. Ta jima zuciyarta na ba ta alamar ta kamu da ƙaunar Bobby. Sai dai take ƙaryata zuciyar tata. Sai a yanzu ne ta gasgata, yanzu da bakin alƙalami ya riga da ya bushe. Ya tafi inda ba a dawowa, har gaban abada. Sans tunani yake shin zai aminta da wasiyyar abokin nashi ne? Ta yaya yarinyar za ta so shi, bayan kuma shi kanshi Bobby ɗin ya faɗa mishi ba wani son shi take yi sosai ba? Amma kuma yana ji a ranshi, ba zai taɓa butulce ma Farouk Sardauna ba. Zai nemi soyayyar yarinyar, matuƙar za ta so shi, to lokacin yin aurenshi ya yi. Zai sanar a gida. Amma dai sai ya fara bin address ɗin ta kamar yadda Bobby ya ba shi, sun haɗu baki da baki sun yi magana, sannan zai sanar ɗin a gida. Amma zai jira har a yi bakwai ɗin Bobby, nan da kwana huɗu kenan, sannan zai je gidan nasu. Kawai dai yau zai kira ta da dare, ya sake maka ta'aziyya, saboda yadda ya ji tana kuka sosai a lokacin da suke yin wayar. Maryama kuwa dolenta ta nemi panadol ta sha, saboda wani irin ciwo da ta ji kanta yana mata. Dukkanin jijiyoyin kan sun ƙulle, sai azabtaccen ciwo da suke sakar mata. Ƙarar wayarta ta ji, ko kallonta ba ta yi ba, saboda ba ta da kuzarin da za ta iya ɗaukar wayar wani. Sai da aka kira har sau biyar, sannan a na shida ta duba mai kiran. Kyakkyawan tsoki ta saki da ta ga Deedah ne ke kiranta. Ta birkita wayar tana faɗin, "Mutum sai baƙar ƙwaƙwa. An fidda min miji ma ba za ka haƙura da kirana ba." Ƙarar shigowar text message ta ji. Ta ɗauki wayar, ta ga Deedah ne ya turo mata saƙo: "Ban kira ki da wata manufa ba Maryam. Ni a tunanina ko auren kika yi ina da darajar da zan kira ki ki ɗauka, ashe ba haka ba ne? To dama ba wani abu ba ne, albishir na kira na miki, cewa mai neman aurenki ya zo, har an yanke magana, Jumu'a mai zuwa za a ɗaura aure." Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke bayan ta gama karanta text ɗin. Tana jin tsananin daɗi a cikin zuciyarta. Allah sarki! Daga Kawu Imrana har Kawu Marwan ɗin ta ji soyayyyrsu ta daɗa ninkuwa a cikin zuciyarta. Dukkaninsu mutanen kirki ne, da suka san daraja da muhimmancin tausayi da soyayya. Cikin ta huɗu a tunaninta ne ya faɗo mata a rai. "Hadiza..." Ta furta a bayyane. "Ban kyauta ba, har yanzu ban sake waiwayarta ba." * Da dare Sans ya kira Maryama, cewa ya kira ne ya ba ta haƙuri kan kukan da ya ji ta fasa ɗazu. Ya mata nasiha sosai, kan haƙuri da ɗaukar ƙaddara. Sosai Maryama ta yi mamaki. Kamar dai ba mugun mutumin nan da ta sani abokin Bobby ba? Wanda fa yake amfani da sunan Annur, yake gidan su Annur a matsayin shi ne Annur. Kai a'a! Ina! Ƙila dai ba shi ba ne. Ƙila wani abokin na Bobby ne daban. Yaushe ya zama na ƙwarai da har ya iya yi ma wasu nasiha haka? * Washe gari Da misalin ƙarfe goma na safe sai ga Alhaji Marwan ya je gidan Kawu Imrana. Dama sun yi waya cewa zai same shi a can ɗin. Yana isowa cikin gida ya kira mai gadin kan cewa ya zo ya buɗe mishi booth, akwai kayan da zai kwaso daga ciki, sannan shi kuma ya nufi part ɗin Kawu Imrana ɗin, kamar yadda ya yi jiya. Ya same shi zaune yana shan coffee. Da faraa Kawu Imrana ya tarbe shi. Musabaha suka yi, sannan ya gwada mishi wuri cewa ya zauna. Taya mishi coffee ɗin ya yi amma ya ce ya ƙoshi, yanzu ya gama karyawa. A lokacin da mai gadi ya fara shigowa da kaya mamaki kawai Kawu Imrana yake yi. Bayan ya gama shigowa da duka kayan ne Alhaji Marwan ya yi gyaran murya sannan ya ce, "To Alhaji Imrana. Wasu ƴan kayayyaki ne dai ga su nan kaɗan babu yawa. Na ga ya kamata a kawo ma amarya, kafin Allah ya ba shi angon lafiya, da kanshi sai ya siya mata. Kuma na tabbata insha Allahu su ma iyayen nashi za su mata. Na ga dai bai kamata a yi aure babu lefe ba ne, shi ya sa na sissiya, babu dai yawa." Cike da mamaki kawu Imrana ke kallon kayan yana yaba kirki irin na Alhaji Marwan. Setin akwati ne mai guda biyar, kalar baby pink.  Murmushinsa ya faɗaɗa kawu Imrana. Ya sake ba Alhaji Marwana hannu suka yi musabaha, sannan Alhaji Marwan ɗin ya miƙe, ya ce, "To Alhaji Imran, ni zan wuce. Office ma nake son wucewa kai tsaye, akwai aiki da ya taso min. Tun jiya da na bar nan gidan na kira wani abokina da yake da babban shago, na mishi bayanin abin da nake so. Sai ga shi yau da sassafe ya kawo kaya, kuma ni kaina na ga ba laifi sun yi kyau sosai. Iya dai wanda suka samu kenan, kasantuwar abun na gaggawa ne, kuma dai duka ba shi ake ma ba. Zaman lafiya tabbatacce ne babban abun so." Bayan ya miƙe tsaye shi ma Kawu Imranan ya miƙe, yana faɗin, "Wannan gaskiya ne Alhaji Marwana. Babu abin da zan ce da kai face na dad'a jaddada maka godiya. Allah ya saka maka da dukkanin alkhairanSa. Su kuma yara Allah ya ba su zaman lafiya, ya ba Annur lafiya." "Ameen ya Rabbi. Ni ina ji sai kuma Ranar Jumu'a ɗin. Da an sauko masallaci da izinin Allah zan ƙoƙarta zuwa, tunda dai sai ƙarfe uku za a ɗaura. Ga wannan." Ya zaro kuɗi daga aljihunsa, ya miƙa wa Kawu Imrana. "Sadakin nata ne." "To masha Allahu! Allah ya nuna mana da rai da lafiya. A gaida iyalin." * Wuraren ƙarfe huɗu sai ga Kawu Imrana ya zo gidan su Maryama. Bayan ya shigo ya zauna ne mai gadi ya shisshigo da akwatunan. Bayani ya ma Mama cewa lefen Maryama ne, daga Alhaji Marwan. Sannan kuma ya labarta mata duk yadda suka yi da shi jiya da suka haɗu. Ta matuƙar jin daɗi, tunda dama a waya ne suka yi magana, cewa ranar Jumua mai zuwa ne ɗaurin auren. Abba ne ya dawo a daidai lokacin. Da faraa suka tarbi juna. Sannan kawu ya koma ya zauna. "Baban amarya." Kawu Imrana ya faɗa, yana murmushi. Tsuke fuskarsa ya yi Abba, bai kuma faɗin komai ba, har Maryama ta wanzu a gabansu, ta ajje musu lemuka da cups a tray. Har ƙasa ta duƙa ta gaishe da su. Ta juya za ta tafi kenan ta jiyo muryar Kawun cike da wasa, yana faɗin, "Amarya ga lefenki nan fa. Surukinki da kanshi ya kawo min su har gida. Ga kuma sadaƙi da kuɗin neman aurenki." Kunya ta ji sosai, ba ta iya furta komai ba, sai kama hanyar barin ɗakin da ta yi. "Zo mana ƴata." Ba musu ta juyo ta dawo, ba ta ɗago kanta ba har ta duƙa a gaban kawun nata. "Ungo wannan." Ya miƙo mata bandir na ƴan ɗari biyar har guda biyu, dubu hamsin hamsin kenan. Cikin alamun tambaya ta miƙa hannu biyu ta karɓi kuɗin. Ba ta samu damar tambayarshi ba, ta ji ya ce, "Dubu hamsin kuɗin neman aurenki ne. Dubu hamsin kuma sadaƙinki. Haƙƙinki ne, ki yi duk yadda za ki yi da su; ƴan hidindimunku na amare, tunda dai angon babu lafiya. Komai naki insha Allahu gobe zuwa jibi za su iso, na yi odarsu daga Dubai, wani abokin kasuwancina da ke can na tura ma. Amma ki yi haƙuri fa, ban tambaye ki irin wanda kike so ba, kuma ƴan matan yanzu na ga su ke faɗin kala ko?" Ya murmusa. "Na tabbata ba zai min zaɓen banza ba. Za ki ji daɗinsu ƙwarai." Hawaye ta ji suna wanke mata kumatu Maryama. Har ma ba ta san ta yadda za ta gode ma bawan Allah'n ba. Mutumin na da kirki sosai, bai taɓa bambanta su da yaran da ya haifa da cikinsa ba. Shi ya sa take jin wata irin kunya na daɗa lulluɓe ta, ta ƙin amincewa da auren ɗanshi. "Insha Allahu zuwa dare, Ahmad zai kawo miki invitation cards, naku na ƴan mata. Sai ku gayyaci duk wanda za ku gayyata, tunda dai biki ne na budurwa ba bazawara ba. Ko zawarawan ma dai ai sun waye yanzu, bikinsu suke yi kamar ƴan matan. Sai dai na canza sunan angon, Muhammad Nuraddeen na ce a rubuta, duka har na ɗaurin aure ma." Gyaɗa kai kawai Abba ya yi. Shi kanshi yana jinjina halin karamci irin na yayanshi. Ba dukkanin yayye ne ke da irin halin Kawu Imrana ba. Bai ma nemi shawararshi ko kaɗan a duk hidimar ba, shi kaɗai ke abin shi. "Ku yi bikinku hankali kwance, kar ki ji komai ƴata. Ai dama ba kowanne biki ba ne ango ke halartar hidimomin, ɗaurin aure ne dai dama ake zuwa, to don wannan mai sauƙi ne, zan iya cewa bai da lafiya ne yana asibiti a kwance." Mama ta duƙa har ƙasa, ta ce, "Allah ya sani, bani da bakin gode maka. Haƙiƙa kai mutum ne na gari, da ke da kyawawan halaye. Allah ne kaɗai zai iya biyanka. Allah saka maka da alkhairi. Allah ya bar zumunci." "Kar ku ji komai fa. Yanzu don na ma ƴata abu har sai an min godiya? Tamkar kaina fa na ma. Yanzu dai, a kaini inda ɗan nawa yake, in gan shi, in masa albishir cewa ya kusa angwancewa." Ya ƙarisa maganar da sakin murmushi mai faɗi. *** *Na gaji.🤣😅* *Na cika alƙawari ko ban cika ba?😀 Na cika. Duk dayake cewa akwai wanda ba su canko daidai ba. Ba zan faɗo ainahin amsar ba, har sai mun zo wurin. Wanda suka canka daidai za su gani, su kuma tabbatar da cewa daidai suka amsa.* *Masu karatu, sai a shirya shan casu, domin kuwa, an kusa zuwa wurin.* *Ba lallai a ji ni gobe ba. Fatan za ku min uzuri.* Thanks all. Pinky durling💞 RAZ 2 [9/13, 8:20 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 6⃣2⃣ Wattpad: Princess Amrah *** Wannan shafin sadaukarwa ne ga Hajiyata Matar Sarki. Fatar dai an haɗa kuɗin ashoben mutane da yawa, don ya kusa ƙarewa...lol. ina yin ki sosai Hajiyata. Allahu ya bar zumunci da zaman tare. Ƙaunarki nake yi fisabilillah. *** Muhammad ne ya musu jagora zuwa ɗakin da Annur ɗin yake. Da shigar su suka same shi zaune ya takure kanshi, yana kallon wuri ɗaya. Ko tunanin me yake oho. Sallamarsu da ya ji ce ya gaggauta ɗago kanshi yana kallonsu. Kyakkyawan murmushinsa mai daɗa fiddo kyawunshi ya sakar ma Muhammad. Shi ma Muhammad ɗin ya sakar mishi murmushin, sannan ya ƙariso daf da shi ya zauna. "Ka ga Kawunmu nan, wanda zai ɗaura muku aure kai da Yaya Maryama. Ga kuma Abbanmu, ai ka san shi ko?" Bai ba Hammad amsar ba sai dariyar yaƙe da ya saki yana bin su da kallo ɗaya bayan ɗaya. Bayan kawu Imrana ya zauna, ya ce, "Ɗana sannu ko? Ya ƙarfin jikin?" A nan ɗin ma Annur bai ce komai ba. Ya sunkuyar da kanshi ƙasa yana kallon wuri guda. "Insha Allahu yau saura sati guda a ɗaura muku aure da Maryama. Ai kana so ko?" Bayan ya rufe fuskarsa ya ce, "Ai Amrah ta ce da ni in so ta, kuma ina son ta ɗin. Ita ma ta faɗa min tana so na." Dariya suka saki su duka, har Abba sai da ya yi dariyar. Saboda yanayin yadda Annur ya yi maganar, dole sai an yi dariya. "Ai haka nake so dama. Insha Allahu za a ɗaura muku aurenku kai da ita. Kana so ka ci gaba da zama a nan ko kuwa dai a fitar muku da gidanku daga kai sai ita?" Shiru ya ma Kawu bai ba shi amsa ba. Don bai ma san inda maganar tashi ta dosa ba. "Tunda ba za ka min magana ba, bari ma in tashi in tafiyata." Jawo rigar Kawu Imrana ya yi, ya ce, "Zan maka magana. Allah kuwa." "To to to na ji. Yi min maganar in ji." Ya dawo ya zauna Kawu Imrana. "Uhm...Amrah fa ba ta da lafiya tun wancan lokacin. Ni ma sai gobe na tuna da haka. Har ma an kai ta asibiti fa. Allah kuwa da gaske nake muku ba ƙarya ba." Gyaɗa kansa ya yi kawu, ya ce, "Allah sarki! To amma dai ta ji sauƙi ai ko?" Ɓata fuskarsa ya yi yana kallon kawu, kafin ya harare shi, ya ce, "Wa ya faɗa maka ta ji sauƙi? Ba ta ji sauƙi ba fa. Haka ma wai aka ce wai ta mutu. Daga farko ban yarda ba. Amma sadda tai min zuwan ƙarshe a mafarki ta sanar da ni hakan, cewa ba za ta sake dawowa ba. Kawai dai in riƙi Maryama a madadinta." Duk da cewa a shirme ya yi maganar, hakan bai hana Kawu Imrana tausaya masa sosai ba. Haka ya ɗan rinƙa jansa da fira, har suka ɗauki tsawon lokaci, kafin ya miƙe, ya ce da su Abba su taso su tafi, yana son tafiya gida, kasantuwar magrib tana gabatowa. * Kamar wasa haka shirye-shiryen aure suka ci gaba da kankama. Ranar litinin ɗin da ta rage kwana biyar aure, Alhaji Marwan ya kira Kawu Imrana a waya, cewa akwai gidanshi da ke nan cikin road K, kusa da nashi gidan. Ba wani babba ba ne sosai, sai a kawo amarya a cikinsa. Sosai kawu Imrana ya yi na'am da hakan. Sannan a ƙarshe suka yi sallama. Lambar wayar Mama ya kira, bayan ta ɗauka suka gaisa, yake yi mata bayanin yadda suka yi da Alhaji Marwan, sannan a ƙarshe ya ce "Kayan Maryama dama sun iso, yanzu haka suna cikin store a ajjiye. Idan an tashi zuwa jere, kawai sai ku faɗa min, zan kira Alhaji Marwan ɗin na sanar da shi." Mama ta ce, "Idan haka ne kuwa ai sai a sanar da shi cewa ranar Laraba za a zo jeren. Gudun kar abun ya cunkushe cikin hidimar biki." Kawu Imrana ya ce, "To madalla. Insha Allahu gobe zan umurta da a kwashe kayan nan ɗin duka a kai su can gidan nata. Kin ga idan an tashi jeren kawai zuwa za a yi." "To babu damuwa Yaya. Ni ɗin ma nan akwai ƴan karikitai da za a kwasa. Su kayan kitchen da bedsheets da labulaye. Jiya muka je da ita duk muka siye su. Goben sai masu kwasar kayan su biyo ta nan su tafi da kayan." "To babu damuwar Hajiyar Maryam. Haka za a yi da yardar Allah." "Na gode ƙwarai Yaya. A gaishe da iyali. Su Hajiya Rakiya dai ai ba sai an kai musu IV ba, saboda su ma masu gayyatar wasu ne." Kawu ya ce, "Wannan gaskiya ne. Za su ji duka insha Allahu." Suka yi sallama. Tana ajje wayar ta ƙwala ma Maryama kira. Bayan ta zo ta ce, "Ga ni Mama." Mama ta ce, "Cikin kayan nan da Hassana Gusau ta kawo miki. Akwai wani na gari na nan a wata roba, ki duba yoghurt na nan cikin fridge, ki tabbatar kin sha fa. Cokali guda za ki zuba garin a cikin rabin cofin yoghurt ɗin. Ki ɗaga kanki ki shanye duka." Cikin jin kunya ta amsa da to, sannan ta juya za ta tafi. Sake kiranta Mama ta yi, bayan ta dawo ta ce, "Matar Sarki ta kira ni ɗazu, ta ce wai ta harhaɗa kuɗaɗen ashoben ƴan RAZ NOVELLA 1&2. To wai tana so ne ki je ki karɓa ki ɗora a motocin haya da za a kai musu. Ita ayyuka sun nata yawa ne. Ga shi kuma jibi ma jere za su je su miki." Duk da dai bakinta cike yake da son yin tambaya amma ba ta yi ba. Haka ta koma ɗakinta tana mai nazartar kalaman Mama. Kenan har an fitar musu da gidan da za su zauna? Zama ta yi a bisa sofa. Ta jawo lakar madubinta, ta ci karo da tarin magungunan da Hassana Gusau ta kawo mata kyauta. Murmushi ta yi, a ranta tana tunanin wanda ake mata shirin domin shi. Mahaukaci ne fa ba mai lafiya ba. A bayyane ta furta, "Allah ya ba ka lafiya ingantacciya Yaa Noor ɗina." * Washe gari misalin ƙarfe huɗu na yamma motar kwasar kayan ta iso ƙofar gidan su Maryama. Baki ɗaya kayan da ke nan ɗin aka kwasa sannan suka wuce kai tsaye GRA, tare da bin kwatancen da Alhaji Marwan ya musu. Suna barin wurin Sans na isowa da motarshi. Ya yi mamakin kiciɓis ɗin da ya yi da motar kaya. To sai ya ƙoƙarta kawar da komai, duk kuwa da cewa zuciyarsa ta ɗan fara kitsa mishi wani abun na daban. A ƙofar gida ya faka motarshi, yana nazarin miye next. Ya ciro wayar Bobby daga jikin chaji, ya latso lambar Maryama, sai dai kuma ya ji ana faɗin babu kuɗi a wayar. Ajiyar zuciya ya sauke, sannan ya jawo tashi wayar da ke jone sautin karatun Qur'ani na fita daga cikinta, ya fara ƙoƙarin kwafar lambar. Babban abin da ya ɗaure mishi kai, sadda ya fara rubuta lambar sai ya ga yana ma da ita, har ya rubuta mata Maryam. Mamaki ya cika shi, nan fa ya fara tunanin inda ya samu lambar. Shiru ya yi na ɗan lokaci, kafin zuciyarshi ta tunasar da shi abubuwan da suka faru kwanaki, da kuma ta yadda aka yi ya samu lambar tata. "Kar dai tunanin da nake yi ya tabbata fa. A ce ita ce Maryama da boka Gagarabadau ya fitar min da soyayyarta ta ƙarfi da yaji daga cikin zuciyata." A bayyane ya yi maganar. Mamaki na daɗa yawaita a zuciyarshi. Me hakan ke nufi? Dama da yarinyar ne Bobby ya yi soyayya kafin ya mutu? Ya aka yi duk ba su sani ba? Kanshi ya jingina jikin sitiyarin motar, yana jin duniyarsa na masa zafi. Raɗaɗi da zugi zuciyarsa ke masa. Ta yaya zai iya cika alƙawarin da ya ɗaukar wa Farouk Sardauna, cewa zai aikata buƙatar tashi ya auri Maryama? Kamar ya saɓa ma zancen boka ne. Dama da ƙyar aka samu aka fitar da soyayyarta daga cikin zuciyarsa. Yana ga matuƙar ya aure ta, lallai soyayyarta za ta ci gaba da haɓaka a cikin zuciyarsa. Duk da dai cewa a yanzu ɗin babu ko kaɗan. Cike da takaici ya tada motar, ya bar harabar unguwar, zuciyarsa na masa zugi. Yana mai tsananin jin haushin dokar da boka Gagarbadau ya gindaya masa, kan cewa babu true love gare shi har abada. * Waya suke da Jiddah, faraa sosai bayyane a saman fuskarta. "Jiddah yanzu don Allah duk irin gajiyar nan da na yi, kuma kina nufin gobe ma sai mun fita?" A ɗaya ɓangaren Jiddah ta ce, "Abu dole. Yo to me muka yi ma? Daga rabon IV fa babu wani abu da muka aikata. Yau fa saura kwana huɗu biki Maryama. Dole gobe mu samu mu rage aiki, ko Salon ne mu fara zuwa. Jibi sai a yi lalle." Ajiyar zuciya Maryama ta sauke. Ta ce, "Oh ni Marryam! Wannan abu ba ya ƙarewa wai?" "Ina fa zai ƙare? Auren kenan ai. Ɗazu ƙawarki Saudat ta kira ni. Take faɗa min wai akwai sauran ƙawayenku na jami'a da ba a kai ma IV ba. To ni dai na ce mata gobe idan mun gama wankin kai, daga can za mu wuce gidansu mu ɗauke ta, sai a kai musu." Guntun tsaki ta saki Maryama. Ta ce "Ni wallahi na gaji da wannan hidimomin. Kuma wai yanzu da zarar an gama, ranar Monday mai zuwa in fara exams." Jiddah ta ce, "To ya za ki yi. Sai haƙuri. Ni dai don Allah gobe ki fito da wuri, yadda za mu yi komai a kan lokaci." "To Allah ya kai mu. Bari in tafi in duba Yaa Noor, duk yau da Hammad kawai na bar shi." Dariya Jiddah ta yi, "Hammad manyan mutane, ƙanin amarya. Sun fa yi hutu ko?" "Ehh mana, sun yi hutu ran Friday ɗin nan. Sai farin ciki yake wai za a yi biki suna hutu." "Gaskiyarsa ai. Biki daɗi gare shi." Daga nan suka yi sallama. Ajje wayar ta yi kan gado, sannan ta nufi ɗakin Annur, zuciyarta cike da ɗokin ganinshi. Bayan ta shiga, ta samu sai yaƙe baki yake, shi kaɗai, yana kallon wuri guda. Gyaɗa kanta ta yi tana murmushi, sannan ta ƙariso gabanshi ta zauna, tana tafa hannuwanta a daidai fuskarsa. Zabura ya yi ya kalle ta, sannan ya kuma sakin murmushi, idanuwansa a kanta. "Sai dariya kake kai ɗaya Yaa Noor. Ba ni labari, me ya faru?" "Hammad ne." Kawai ya faɗa, yana ci gaba da murmushi. "Me ya yi Hammad ɗin?" "Ya ce wai gidanmu daban za a fitar mana, daga ni sai ke idan an mana aure." Gyaɗa kanta ta yi. Ta ce "To kai ka ji daɗin hakan ne?" Harararta ya yi, ya ce, "Ehh mana. Na ji daɗi sosai." Sai kuma ya ɗaure fuska, hawaye na ƙoƙarin saukowa daga idanuwanshi zuwa kumatunshi. Ganin yadda idonshi ya cika taf da ƙwalla ya sa hankalinta ya tashi. Ido a buɗe take tambayarshi, "Me ya faru kuma don Allah? Na rasa me ya sa sam kuka ba ya maka wahala." Hannunshi na dama ya sa ya share hawayen. Ya ce, "Don Allah kar ki tafi ki bar ni, duk wuya duk rintsi. Kin ga Amrah ma sai da aka kusa bikinmu sannan ta tafiyarta ta barni, ta bar rayuwata baki ɗaya." A daidai wannan lokacin sosai kuka ya ci ƙarfinsa. Ya haɗa kansa da guiwa, yana mai shessheƙar kuka. "Yah Noor ya akai ka san haka? Ta ya aka yi ka san cewa sai da kuka kusa aure sannan Amrah ta tafi ta bar ka? Kenan hakan na nufin ka fara tuno wasu abubuwa na rayuwarka?" Bai ce da ita komai ba, kamar yadda ba ta tsammani zai ce ɗin ba. Sai dai kuma mamaki take. Tana kuma ƙara tabbatar da lallai sauƙi na zo mishi. Duk wasu shirme da yake yi a baya sun sauƙaƙa. Wani abun ma idan ya yi shi ba za ka taɓa cewa shi ne ba. Ga kuma yanayin kayan da mai gadi ke saka mishi. Tsafta sosai. * Tun daga sadda ya kula da fitar Maryama. Ya lallaɓa a hankali ya shiga ɗakinta. Cikin nasara ya samu wayarta a kan gado, ba ta fita da ita ba. Da sauri ya ɗauka. Ya ja pattern ɗin da ta saka, babu ɓata lokaci wayar ta buɗe. Neman lambar Maman Abdul ya hau yi, amma bai gani ba, saboda bai san sunan da ta saka mata ba. Hakan ya sa ya koma a farkon contacts ɗin, ya rinƙa bi a hankali ɗaya bayan ɗaya, har ya zo kan lambarta, ashe Dr. Islam ta saka mata. Lallaɓawa ya yi ya fice da ɗakin, yana tunanin yadda suka yi da Maryama jiya. Ya same ta da IVs a gabanta, yake tambayarta ta gayyaci Maman Abdul kuwa? Ta ce da shi ba ta gayyace ta ba, ba kuma za ta gayyace ta ɗin ba. Ya roƙe ta kan ta taimaka, amma ta ƙiye masa. Ita kuwa tana gudun tonuwar asiri ne kawai, ko kaɗan ba za ta so Dr. Islam ta san da zancen auren ba, don kar ta zo ta nemi sanin mijin. Kuma ma ta san halin Hammad da surutu, da kanshi zai iya jan ta ya kai ta har ɗakinshi, inda Annur ɗin yake. Gatsine ya yi haɗe da latsa kiranta, bugu biyu kuwa ta ɗauka, da sallama ƙunshe a bakinta. Amsa sallamar ya yi da murmushi ya gaishe ta. "Muhammad yarona ya kake?" "Lafiya lau Aunty. Ya Abdul?" "Abdul na lafiya Hammad. Ya Mama da Maryam?" "Suna lafiya duka Aunty. Dama kiranki na yi na ba ki wani labari." Murmushinta ta faɗaɗa, sannan ta ce, "To ina saurarenka yarona." Sai da ya lelleƙa ko'ina irin yadda magulmata ɗin nan suke yi. Kafin ya ce, "Ko kin san kuwa an kusa yin auren Yaya Maryama?" Da mamaki Dr. Islam ta ce, "Aikuwa dai ban sani ba. Amma yaushe ne auren da Maryama ta gagara ta sanar min?" "An kusa fa Aunty. Na ji an ce wai ranar Friday ne ɗaurin auren. Amma dai ranar Alhamis za a yi Get Together a gidan Kawunmu." Mamaki sosai Dr. Islam ta yi. "Muhammad kodai wasa kake min? Ta yaya Maryama za tai aure har ma a ce kwanaki huɗu kacal suka rage kuma ba ta sanar min ba?" Ɗan taɓe bakinsa ya yi Hammad. Ya ce, "Allah kuwa da gaske nake yi Aunty. Amma ki kira ta anjima sai ki tabbatar. Kar fa ki faɗa mata na kira ki." Dariya ta yi sosai. A ranta tana mai jinjina wayo irin na Muhammad. Idan ya yi wani abu sai a ce ya zarce shekarunshi. "Ba zan faɗa mata ba insha Allahu. Kai ma kuma sai ka kame bakinka to. Zan san yadda zan yi." "Yauwa Aunty. To ki gaishe min da Abdul. Idan za ki zo bikin don Allah ki zo min da shi. Zan yi party ni ma ɗin ranar Alhamis." "To na maka wannan alƙawarin, insha Allahu. Ai har ma da Momynmu za mu zo da yardar Allah. Sai anjima ko." Ta katse kiran. Har zai koma ya miyar da wayar kuma sai ya tuna da ranar da ya kira Kawu Imrana ɗin nan fa ya manta bai goge ba. Don haka yanzu kam dole sai ya goge. Ya sakar ma kanshi murmushi, haɗe da yin delete na kiran. Har ya miyar da wayar Maryama ba ta dawo ba. Sosai ya ji daɗi, koba komai zai ga Abdul ɗinshi, zai zo wurin partynshi. * Tun sadda ya koma gida yake jin zuciyarsa na masa zafi. Ya ma rasa me zai yi ya ji daɗi? Baki ɗaya duniyarsa ta juye masa. Babu ko kaɗan ɗin farin ciki a cikinta. Ga shi dai bai rasa komai na game da dukiya ba. Gadonshi da yake kwance a kai, babba ne sosai, mai ɗaukar aƙalla mutum uku ko huɗu. Sanyin AC ya gama garwaye ɗakin, ga wani irin ƙamshi da ke fita ta kowacce kusurwa. Bai rasa dukkanin kayan more rayuwa ba, amma kuma farin ciki ya masa ƙaura. Lallai ya yarda, cewa dukiya da kayan more rayuwa ba koyaushe ne suke zama dukkanin farin cikin mutum ba. A cikin ɗan taki kaɗan, komai ya juye masa. Kullum cikin ƙunci da baƙin ciki, tun daga mutuwar babban abokinsa. Sosai yake tunowa da iyayenshi, da kuma danginshi; na uwa da na uba. Ko ya suke yanzu? Ya dai tabbata cewa iyayensa basa raye. Amma kuma ya san ba lallai ba ne a ce duka har danginshi babu su ba. Dole za a samu wanda suke raye. Tunani yake a ransa, shi yanzu a haka rayuwarsa za ta ci gaba, ba tare da wani makusancinshi na tare da shi ba? Ya sani, ya san cewa babu abin da ya rasa a gidan da yake. Haka kuma ko sau ɗaya ba su taɓa yin wani abu wanda zai nunar da cewa sun gane cewa ba shi ne ɗansu ba. Amma kuma yana ji a ranshi, lallai duk daren daɗewa sai asirinsa ya tonu. Sai sun fahimci cewa ba shi ne asalin ɗansu ba. Juyi ya sake yi, yana jin yadda ruwan hawaye ya wanke masa dukkanin fuskarsa. Me ya sa rayuwa za ta masa haka? Mafita yake nema daga wurin Allah, yana fatan Allah ya kawo masa ɗoki, ya fitar da shi daga wannan damuwar da yake cikinta. Duk yadda yake son cika alƙawarin da ya ɗaukar ma Farouk Sardauna dole hakan ba zai yiu ba. Zai haƙura, ba zai taɓa kai kanshi ga auren Maryama ba, gudun faruwar wani abun. Har aka fara kiran assalatu ko kaɗan Sans bai runtsa ba. Ya ma gaji da kwanciyar, a ƙarshe ya tashi zaune, yana kuka sosai, wanda har muryar kukan ma ta disashe. Da na sani kawai yake daɗa yi, wanda ya zame masa tamkar abinci. Tun daga sadda Bobby ya rasu kullum cikin takaicin rayuwarsa yake. Munanan halin da suka aikata, har Bobby ɗin ya rasu a cikinsu. Tashi ya yi jiki babu kuzari, ya nufi ban-ɗaki. Alwalla ya ɗauro sannan ya dawo, ya shimfiɗa dardumar sallarsa, ya fuskanci alƙibla, haɗe da kabbara sallah. Ya daina wasa da salla, kwata-kwata. Sosai yake kasƙantar da kanshi ga mahaliccinshi, yana mai neman yafiyar Allah, tare da roƙawa abokinsa gafarar Allah. *** *Da gaske Sans na ba ni tausayi, har cikin zuciyata. Idan na tuno da yadda ya yi rayuwarsa a baya, da kuma yadda ƴan ta'adda suka salwantar da rayuwar makusantanshi, sai in ji duk wata tsanarsa da nake tana wucewa. Akwai wasu daga cikin masu karatu, wanda suke cewa wai bai kamata Sans ya tuba ba, sai dai ƙarshensa ya yi mummuna. Ba zan faɗi komai a yanzu ba, don kar na ba ku satar amsa. Sai dai kuma ina so ku sani, komai na duniyar nan yana da sila. Idan Farouk Sardauna ya yi silar lalacewar Sans, to kuma ga shi mutuwar Farouk Sardauna ta yi silar shiryuwarshi. Abu ɗaya tal ya rage na rayuwarshi, wanda sannu a hankali duk zan warware muku. Da ni da ku duka, babu wanda ya fi ƙarfin faɗawa a irin halin da Sans ya faɗa, domin kuwa babu wanda ya fi ƙarfin ƙaddara. Addua dai ce takobinmu, ita za mu riƙa, muna fatar Allah ya tsarkake mana zukatanmu, mu kasance masu kyautata rayuwarmu, har sadda mutuwarmu za ta zo ta ɗauke mu.* *Daga nan kuma sai ku taya ni wangale baki, na jeren da za a je gidan Marnoor. Abun fa da gaske ne, biki sai daɗa kusantowa yake. Abun ya zo, inji mai tsoron wanka.😁🤣* *Me za ku ce game da wannan surutu da Hammad ya yi? Shin ya kyauta ko kuma bai kyauta ba? Akwai fa ƴan bayan Hammad, masu yin ƙani da shi, wanda na san kai tsaye za su ce ai Hammad ya musu daidai😀. Yaro mai surutu fa haka yake. Akwai sadda yake yin mai maana, kamar sadda ya kira kawu Imrana. Akwai kuma sadda yake yin mara maana, wanda shi ne ma ya fi rinjaya. Ga shi dai Hammad ya kwafsa, ya kwaɗawa Dr. Islam kira ya sanar mata auren Maryama. Ko ya abun zai kaya? Za ta zo ko ba za ta zo ba? Akwai fa cakwakiya.😊😅* *Nagode ƙwarai masu bibiyar wannan labarin. Har ma wasu lokutan nakan rasa abun faɗe, tsabar faranta min rai da masoyana suke yi. Wasu groups ɗin da bana ciki ma, ina jin labarin yadda suke ƙaunar ANS. Akwai lokutan da ake min Copy and paste na yadda ake hirar ANS. Ban san da bakin da zan gode muku ba. Sai dai addua da fatar alkhairi. Allahu ya bar zumunci, ya saka muku da dukkanin alkhairanSa. I love y'all, fisabilillah.* Pinky durling💞 RAZ 2 [9/14, 5:33 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 6⃣3⃣ Wattpad: PrincessAmrah *** Washe gari tun da safe misalin ƙarfe tara na safe ƴan jere suka tafi domin aiwatar da aikinsu. Maryama kuma dama mukullin ɗaya motarsu a hannunta yake. Tare da Hammad suka tafi, bayan ta shiga sun gaisa da Annur, ta ba shi duk abin da ya dace na kalacinsa. Kai tsaye gidan su Jiddah suka dosa. Daga nan suka wuce wurin Salon. Ba su wani tarar da layi ba. Mutum baiyu ne a gabansu. Hakan ya sa misalin biyu na rana an gama musu duka. Daga nan suka wuce gidan su Saudat. Sun samu ta shirya su kawai take jira, da yake sai da Jiddah ta kira ta ce ta zama cikin shiri, sun kusa zuwa su ɗauke ta. Sai da suka yi sallah, har abinci Saudat ta zubo musu sannan suka bar gidan, suka nufi kakkai ma wanda ba su kai ma kati ba. Har kusan biyar na yamma sannan suka gama. Bayan sun kai Saudat gida sannaam suka wuce kasuwa domin yin siyayyar da ba su kammala yi ba, ta Get Together. * Tun sadda Kawu Imrana ya kira shi cewa ƴan jeren sun isa gidan, yake tunanin yadda zai yi da su ta ɓangaren abinci. Ga shi kuma ba ya son iyalinshi su san da zancen auren ko kaɗan, kamar yadda ya yi ma kawu Imrana alƙawari. Hakan ya sa kawai ya yanke hukuncin zuwa Restaurant ya musu odar abincin komai yawan shi. Falon nata ya shigo bai same ta ba, hakan ya sa ya gyaɗa kanshi haɗe da hayewa sama. Ya rasa ko wace irin mace ce ita ɗin. Sam ba ta son mutane. Ko a falonta ba ta cika zama ba bare cikin masu aiki. A ranshi yake cewa dama haka Shuwa suke, ko kuwa dai ita ɗin ce haka? A kan Sofa ya same ta riƙe da wayarta, ta miyar da dukkanin hankalinta ga wayar. Har ya ƙariso ya zauna a gabanta ba ta san ya iso ba, sai da ya yi gyaran murya sannan. Da murmushi take kallonshi, bayan ta saka wayar a duhu. Murmushin ya sakar mata shi ma, ya ce, "Wane irin littafi kuma ake karantawa yau?" Cike da soyayya take kallonshi, ta ce, "Har ma ka san littafi nake karantawa kenan." Hannunta ya kama ya riƙe, ya ce, "Dole in sani ai, saboda aikinki ne. Ya sunanshi, faɗa min? Wata ƙila idan sunanshi ya min ma kin ga kawai sai ki karanta min." Sai da ta ɗan yi far da ido kafin ta ce, "Sunanshi WANDA YA DAKA RAWAR WANI...Labari ne a kan wata yarinya Farha, wacce ta shiga gararin rayuwa, ta dalilin ƙawa da kuma namiji. A ƙarshe ta faɗa harkar karuwanci, inda tun a duniya ta girbi abin da ta shuka. Marubuciya Maimuna Bashir Miemie Queen ce ta rubuta shi." Gyaɗa kansa ya yi, ya ce, "Allah sarki! Har na ji ta ba ni tausayi. Yo wannan rayuwar ta yanzu ka ɗauke ta da sauƙi ma ya ka ƙare bare kuma ka zafafa ta? Allah dai ya shige mana gaba, ya yi mana jagoranci a dukkanin lamurranmu." "Ameen." Ta faɗa tana kallonshi. Yarinyar da ke kwance bisa gado tana barci ya kalla, ya bi a hankali ya cire mata takalmin ƙafarta, ya ce, "Wani abu sai Shereefa. Wato in dai ba barci ta yi ba ba a taɓa raba ta da takalma." "Kai ma dai ka faɗa. Ai ni kam ban san kalar Yesmeen ba. Sosai ta gado Yaya Salman. Aunty ta sha ba mu labarin yadda ya yi yana yaro. Ko kaɗan ba ya yarda a raba shi da takalma. To ga mai gadon shi nan ya samu ai." Miƙewa ya yi tsaye, ya ce, "Ni zan fita, wata ƙila daga Office akwai inda zan wuce. Ban ma dai yi niyyar zuwa Office ɗin ba gaskiya, saboda na tashi jikin ba daɗi. Wani dalili ne mai girma zai fidda ni." Miƙewa ta yi ita ɗin ma, suka ci gaba da taku tare, har suka sauko daga bisa bene. A falo ta mishi sallama da fatar alkhairi, sannan ya fita, ita kuma ta nufi ɗakinta. * Wuraren ƙarfe shida na yamma ƴan jere suka koma. Fuskokinsu a sake, dangin Mama ne da kuma na Abba, da yake kansu a haɗe yake, akwai kyakkyawar alaƙa a tsakaninsu. Da faraa Mama ta tarbe su, ta ce, "Sannunku da dawowa. Har an gama kenan. Sannu, sannunku da aiki." Amsa mata suka yi, wata babbar mace daga cikinsu, wacce ta kasance Yaya ce ga Mama, ta ce, "Gaskiya ba laifi Maryama ta yi sa'ar dangin miji. Domin kuwa wani mutumi yadda ya rinƙa hidima da mu abun sai godiya. Akwai kirki sosai wallahi. Gaskiya ki ce da Alhaji Balarabe ya jaddada mana godiya a gare su, domin kuwa ba kowa ba ne zai iya yin wannan hidimar." Mama baki a sake ta ce, "Aikam zan faɗa masa insha Allahu." Daga nan suka fara haramar tafiya. Da zummar wasu idan suka zo gobe sun zo kenan har sai bayan biki. A gajiye Maryama ta dawo gida ita da Hammad. Sai da ta fara zuwa inda Annur ta ɗan jima kafin ta dawo ɗakinta, ta watsa ruwa sannan ta saka kayan barci, a daidai sadda ake kiran sallar magrib. Zumbuleliyar hijabinta ta zumbula, sannan ta kabbara sallah. * Tun da sassafe mai lalle ta iso. Ƙarfe goma na safe ne dama aka saka za a yi sa lalle. Daidai lokacin kuwa gidan ya fara ɗaukar harama. Ƴan mata duk sun zo domin gabatar da sa lalle. Wanda shi kanshi ɗin akwai wani ɗan guntun casu da za a yi bayan laasar, a lokacin an gama yi ma kowa lallensa, tunda ita amarya dama sai da dare za a mata, sadda duk aka warwatse. Jiddah da Saudat kuwa gidan suka dawo da zama daga yau, saboda za su fi jin daɗin hidimar, da kuma aiwatar da komai a kan lokaci. Da yamma kuwa aka ƙawata gidan da simple decoration, kalar Pink and gold. Wurin ya yi kyau sosai, aka jera kujeru, da kuma gefe guda da aka ajje royal chair, wacce amarya za ta zauna a kai. Ƴan RAZ NOVELLA da kansu suka ɗauko Ado Gwanja, wanda musamman saboda ranar yau zai zo ya nishaɗantar da su. Har Gwanja ya iso harabar wurin amarya da ƙawayenta ba su fito ba. Bai damu da hakan ba, kawai ya fara sakin kiɗa. Sautin na tashi tamkar an tsakuri ƴan Nagarta Fans Group ne. Ummu Aysher ba ta ko ƙarisa naɗin ɗankwalinta ba ta fito, gyale a hannunta tun daga bakin ƙofa take rawa, har ƙasa-ƙasa take yi. Mienerh ce a bayanta, sun haƙiƙance tsakaninsu da Allah rawa suke, har suka iso harabar da Gwanja ɗin yake. Aikam yana ganinsu ya canza salo, aka sako wakar A sha rawa rawa. Kafin ka ce kobo fili ya cike da ƴan mata, ƴan group group sai cashewa ake, har lokacin da Jiddah da Saudat suka fito da amarya. Aunty Maijiddah Musa ce biye da su a baya, sai famar sakin murmushi take, tana ɗan taka rawar dattako, irin ta manyan mutane. Amarya ta sha gayunta, cikin dressing kalar golden.  Da haka dai Ado Gwanja ya nishaɗantar da su, ƙarfe shida da rabi na yamma aka gama. Cike da nishaɗi aka warwatse. * Da dare mai lalle ta hau zana ma amarya nata lallen, inda Maryama ta ce ita kam ba ta son mai yawa, ta fi son kaɗan irin wanda ake yayi yanzu.   Sai kusan sha ɗaya na dare sanann suka sallami mai lallen ta tafi. * Ranar alhamis da safe aka fara shirin yin walima, inda aka gayyaci Malama Zulaihat Rano da aminiyarta Khadija S Mohd suka gabatar da waazi mai ratsa zukata. Sosai suka jawo hankalin amarya a kan ladabi da biyayya ga mijinta. Amarya ta sha kyau sosai, inda ta sha bakin dressing abunta.     Sosai aka ci aka sha a wurin wa'azin. Ba wai amarya kaɗai ba, har ma da sauran mutane sai da suka girgiza da yadda malaman suka rinƙa tsoratar da amarya daga zaluntar mijinta. Suke hasasho mata rahama matuƙar ta kyautata ma mijinta. Sai sha biyu na rana sannan aka gama wa'azin, saboda da yamma kuma za a yi Get Together a gidan Kawu Imrana. Wanka ta yi ta saka wata ƴar ƙaramar riga iya guiwa. Rijif! Ta faɗa bisa gado, tana faɗin, "Kuma wai fisabilillahi anjima wani abun za a sake yi. Ni wallahi in da za ku bi ta tawa da an fasa. Na gaji sosai." Harararta Jiddah da Saudat suka yi, Jiddah ta ɗika mata dukan wasa, ta ce, "Lallai ma yarinyar nan kin raina mutane. Ai in Allah ya yarda Party an yi shi an gama. Gwara ma ki saka a ranki cewa babu fashi, da izinin Allah. Bari ma ki ga in kira matar nan mai make up, kar ta ɓata mana lokaci, shi ya sa na so kar ta tafi ɗazu amma ta nace wai da wuri za ta dawo." Ta latsa kiran mai kwalliyar. Bugu biyu kuwa ta ɗauka, Jiddah ta ce, "Dama ce miki zan yi don Allah ki taimaka mana ki zo da wuri. Wallahi ba ma so a yi dare ne. Get together ne fa har da iyaye duk za su je. So muke amarya ta shirya da wuri, in ya so duk wacce ba ta shirya ba sai a yi babu ita." Mai make up ɗin ta ce, "To insha Allahu da an yi sallar azahar zan zo. Kar ki ji komai." "To shi kenan, sai kin zo." Ta tsinke wayar tana faɗin "Oya tashi ki yi alwallah, yadda idan lokacin sallah ya yi yi kawai za ki yi. Ni fa kin san ni da uzurta mutum, don ba na son ɓata lokaci a komai nawa." Tashi ta yi Maryama, ta ce, "To Aunty Masifa." Ta nufi ban-ɗaki. "Na dai ji koma me za ki ce da ni ki ce. Ni ma wankan zan yi yanzu. Bara na je na fara faɗa ma dattawan can, su taimaka su shirya da wuri su ma. Don na yi waya da Yaya Deedah, ya ce ƙarfe biyar daidai za su zo da motocin kwasar mutane." Saudat da ta miƙe kan gado ta ce, "Ai kin san su manyan mutane ba su cika ɓata lokaci da yawa ba. Matsalar dai dama daga ƙawaye ne. Amma da yake mun jaddada musu cewa da wuri ne na san insha Allahu za su je da wuri ɗin." "To Allah ya sa." Sannan ta nufi fita zuwa ɗakin Mama. Maryama na fitowa wayarta na fara ruri. Koda ta duba ta ga sunan Dr. Islam ne. Da hanzari ta goge jiƙar da ke a hannunta sannan ta ɗaga kiran da sallama a bakinta. "Habawa Maryana. Ai wallahi kin ba ni mamaki." Furucin da ta ji Dr. Islam ta yi kenan, ba tare da ko saallamar ta amsa ba. "A yi haƙuri Aunty Islam, duk da dai ban san me na yi ba amma dai na ɗauki laifina." "Hmm! Na ji to. Ya shirye-shirye?" Cikin faɗuwar gaba Maryama ta dafe ƙirjinta, da rawar murya ta ce, "Na me fa?" Gyaɗa kanta ta yi Dr. Islam tamkar tana a gaban Maryama ɗin ne. Ta ce, "Aure za ki yi Maryam amma ko ki sanar mana? Maryam amana ba ta ce haka ba. Tamkar ƙanwata ta jini haka na ɗauke ki. Amma da alama ke sam ba ki ɗauken tamkar yayarki ba." Sosai bakin Maryama ya ɗinke. Ƙoƙarin tattaro magana take amma ta kasa. Sai famar muzurai take kamar wacce ta yi ƙarya aka turke ta. "Dole za ki yi shiru ai. To duk da dai ba a gayyace mu ba muna nan zuwa anjima ni da Momy da yaronki. Za mu zo matsayin gayyar nagayyaro." "Uhm...Aunty Islam kina ji na? Wallahi ba haka ba ne. Komai da komai a cikin ƙurewar lokaci ya kasance. To ni kuma ba na so na tayar muku da zaune tsaye. Wannan dalilin ne ya sa ban sanar muku ba. Don Allah a gafarce ni, insha Allahu ba zan kuma ba." Dr. Islam ta ce, "Uhmmm! Kamar da gaske, sai wani marairaicewa take. To na ji. Sai ki turo min address na inda za a yi. Kuma ki ce da angon ya tanadi kalaman da zai kare ki a wurina idan na zo. Ina jiran text na address ɗin yanzu." Ba ta jira Maryama ta sake faɗin komai ba ta tsinke kiran. Da ƙyar ta haɗiyi yawu Maryama. 'To a ina suka ji?' Tambayar da ta ma kanta kenan. Hammad ya faɗo mata a rai. A zahiri ta furta, "Tabbas idan ba wurin Hammad ba babu inda za ta ji. Amma wannan yaro ya iya tsiya. Har sai da na ce da shi ya kame bakinsa fa." Saudat ta ce, "Maganinki kenan ai. Nikam Hammad ya min daidai. Ban ga dalilin da zai sa ki ƙi faɗa mata ba ai, duk da ban santa ba." Ta sake gyara kwanciyarta. A daidai nan Jiddah ta dawo. Tun daga bakin ƙofa take faɗin, "To wallahi manya dai sun ce daga gare su babu matsala. Tunda dai already sun yi wankansu tun na waazi ɗazu. Matsalar daga gare mu take. Na ce da su insha Allahu babu damuwa. Komai a kan lokaci za a yi shi. Tunda dai har wurin can an kimtsa komai." "Wurin wa kika ji an kimtsa komai?" Maryama ta faɗa tana shimfiɗa dardumar sallah a ƙasa. "Yaya Deedah ne ɗazu da yake jaddada min cewa da wuri za a zo kwasar mutane ya ce an gama decoration, kuma ya yi kyau sosai." Cikin taɓe baki Maryama ta ce, "Ni dama da shi kika daidaita kawai." Harararta Jiddah ta yi. "Yar rainin hankali. Sai aka ce miki rasa masoyi na yi da za ki min ƴan kwashe-kwashe?" "Ba wani kwashe-kwashe ai. Tun sadda kuna waya ɗazu ai na fara fahimtar wani abu. Wannan wasa da dariya haka." Saudat ce ta jeho wannan maganar. Ta miƙe zaune. Bayyanannen tsaki Jiddah ta yi, ta ce, "Duk ba ni da lokacinku." Ta shiga toilet abun ta. * Bayan an gama shirya Maryama, sai da ta fara shiga ɗakin Annur, a lokacin duk an gama kwashe mutane, daga Jiddah sai Saudat ne kawai a gidan, sai mai gadi kawai. Har Mama ma danginta sun ce ba za a barta a gida ba. A gabanta za a yi komai. Rusunawa ta yi ƙasa tana fuskantarshi, har ƙamshin turarenta na dakar hancinsa. Cikin wani irin salo yake sakin tattausan murmushi, mai cike da soyayya da ƙauna. Ya haɗe tafukan hannayensa a wuri guda, yana fuskantarta ido cikin ido. Ji ta yi baki ɗaya ya gama tsuma ta da ƙaunarsa. A haka da ba yi da hankali yake mata irin wannan kallon na soyayya, to ina ga ya samu lafiya? "Yah Noor za mu tafi, wurin event na bikinmu. Will you say something, please?" Shiru ya mata, amma har yanzu bai daina sakin murmushi ba. "Say something Yah Noor, please. Yau na ɗaya daga cikin ranaku masu muhimmanci a rayuwarmu. Na so a ce kana a cikin hankalinka, ka halarci wannan rana. Sai dai kuma kash! Allah bai nufa ba, haka Ya tsara ma rayuwarka. Ka kwantar da hankalinka, Allah ba mantawa ya yi da kai ba, sannu a hankali za ka samu lafiya, za ka warke ka dawo da cikakken hankalinka." Hannunta na dama da tun shigowarta yake kallonshi, ya kama ya riƙe. Daidai tafkeken zoben zinarin yatsarta ya kai hannunsa, a hankali ya zaro shi, ta ci gaba da binsa da kallo. Bayan ya fiddo, ya kawo shi kusa da idonshi yana binsa da kallo. Tamkar ya san zoben, haka ya ji. Wani irin sara ya ji kansa ya masa, a lokacin da yake kallon zoben. Kamar zai tuna wani abu game da shi, sai dai kuma ya kasa tunawa. Ɗan taunar leɓonsa na ƙasa ya yi, sannan a hankali ya miyar mata da zoben daga yatsar da ya fiddo shi, ya miyar mata, ya zauna kuwa daram. "Time is going Yah Noor. Will you let me go?" Bai san me zai faɗa mata ba, haka kawai ya samu kansa da ɗaga mata kai, yana sakar mata tattausan murmushi, duk da cewa har yanzu bai daina jin kansa na sara masa ba. Tashi ta yi da sauri ta tafi, tun daga nesa take faɗin, "Am so sorry Babes. Kuna ta jirana ba? Ga ni na iso." Fitowa suka yi Jiddah na riƙe da purse ɗin Maryama a hannunta. A harabar gida suka tarar da Deedah ya yi zaune a mota, yana jiransu. Sosai yake kallon Maryama, yana jin yadda wutar ƙaunarta ke daɗa kunnuwa a cikin zuciyarsa. Amma ya zai yi? Dole ya ƙoƙarta fitarwa ko ba ya so. Saboda ya sani, Maryama ba za ta taɓa zama ta shi ba. Murmushi ya saki bayan ya fito daga motar. "Amarya, you know what? Kin yi kyau sosai, lemmi snap you before we leave." Ya hau ɗaukarta hoto, da Iphone X ɗinsa. Sai da ya mata da yawa, sannan suka shisshiga motar, Jiddah na zaune a gaba sai Maryama da Saudat a baya. Sadda suka isa gidan su Deedah, Maryama da Saudat ba su fita ba, sai da Jiddah ta je ta sanar cewa ga amarya nan ta iso. Ƙawaye wanda suka yi ashobe su fito, za a shigo da amaryar. Sauya kiɗa aka yi, yayin da amarya ta fito daga motar, aka yi jeri kowacce ƙawa da partner ɗinta, amarya kuma na daga tsakiya, sai Hammad da Abdul-Ahad biye da ita a tsakiyar, saboda Hammad ya ce ba za a yi babu su ba. Isowarsu harabar gidan, sautin ya ƙara tashi, yayin da mutane suka mimmiƙe tsaye, cike da farin ciki ana tattafawa. Yadda aka tsara wurin kanshi abun kallo ne. Decoration ɗin wurin kalar yellow aka yi, an jera kujeru masu matuƙar kyau.  Har gaban kujerar amarya suka raka ta. Sai da ta zauna sannan masu hoto suka hau yi, masu video kuwa dama tun fitowarta daga mota suka fara. Wuri ya yi wuri fa. Domin kuwa taron mutane maabota karatun Hausa Novels ne jere, wasu ma sai ka yi mamakin ta yadda aka yi suka ji. Laakari da yadda bikin ya zo, a gaggauce aka yi komai. Hotuna ake sosai, uwar amarya ma ta taso aka musu, dangi da ƴan uwa har da ƙawaye, sai shan hotuna ake. Da ƙyar MC ya roƙe su suka watse, sannan aka ci gaba da gudanar da partyn. An yi nisa sosai ne MC ya ce, "Ga Princess Amrah nan za ta fito, za ta rera mana tata waƙar da ta yi musamman saboda ango da amarya." Nan fa aka hau tafawa. Ana jiran isowar Princess ɗin. Cikin taku mai nutsuwa ta iso, tana sanye da wata doguwar riga kalar pink, wacce ke ja har ƙasa. Ta sha ɗaurin ɗankwalinta mai matuƙar kyau, da make up na ji da gani. Ita ce a gaba, sai ƴan RAZ NOVELLA bayanta sun jera layi. A hankali sauti ya rinƙa tashi, nan fa suka hau takawa cikin rawa mai kyau. Waƙar ta fara rerowa, tana faɗin, "Biki wan shagali, Eh biki wan shagali, ake a yau gidajen girma, Maryama da Annur masoyan asali. Farko da sunan Rabbi ubangiji maqagin halitta, Shi ne ya bani damar da nake zubo dukkan hajata, Daɗo dubun salati ga Annabin gaban duk halitta, Da alihi sahabbansa a kullum suna yin ƙyalli. Wannan waƙar aure ce nake a yau ba ƙyashi, Ga wanga ango da amarya suna ta yin ƙamshi, A duk ta inda na gitta wannan bikin ina yin son shi, Domin ko ƙaunar junansu suke ta yi tun asali. Ga dandazon mutanen arziƙi fa duk sun zozzo, Farko Nagarta Writers na hanga sun zo, Sai Raz Novella a gefe murna suke har da ƙwazo, Nagarta Writers Fans group ƙaunarsu yau sun furzo, Ga wannan aure rawa suke ta yi ga ƙyalli. MH fans na gaishe ku a wannan waƙar tawa, Queen group of Novels ku marmatso ku yi rawa, Ga Lubbatu's Crew ma na gansu suna takawa, House of Novels ma a gefe murna suke ba misali. Pherty Novels gaishe ku nake a yau kun ji ni, Asisi Fans Club ma na gaida ku fa ba bimbini, Zauren Sadeeya Novels ku Marmatso nan ga ni, Ƙarshe na sa ƴan Meesha group novels kun hau tubali. Wattpadians ga taku fa gaisuwar ku yo amsawa, Dukkan mutuncin nan da kuke yi min ina jinjinawa, Comments da votes ɗin naku ku ƙara yo ninkawa, Masoyiyarku fa Amrah Princess ce mai ƙyalli. Sauran groups da dukka nake kuna cikin ruhina, Na san kuna son auren Annur da Maryama ku nuna, Ni ma ina ƙaunarku da gaske cikin ƙalbina, Maryam Indabawa group Chart ƙaunarku nake yi tun asali." Tana kaiwa nan suka rinƙa rawa sosai, har ƙasa-ƙasa suke duƙewa. Amarya Maryama da ƙawayenta suka hau yin liƙi, saboda sun ji daɗin yadda Princess ta waƙe amarya da ango. Duk da cewa Dr. Islam ta yi mamakin sunan angon da ta ji an faɗa, sai ba ta kawo komai a ranta ba, aka ci gaba da cashewa. *** *Ban yi tunanin shafin zai kai har tsayin haka ba. Sai ga shi kuwa ya kai.* *Akwai muhimmin abu da na warware a cikinsa. Wa zai canka?* *Well...😀 kun ga mun gangara ɓangaren nishaɗi ko? Kar dai ku shagala, akwai cakwakiya da dama nan gaba. Tahm.* Thanks all. Pinky durling💞 RAZ 2 [9/15, 8:06 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taɓa zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 6⃣4⃣ Wattpad: PrincessAmrah *** Sai dare sannan aka tashi daga Partyn. Sosai duk wanda ya halarci wurin ya yi enjoying ɗinsa, barinma ƙawayen amarya da suka sha casu wanda suka jima ba su yi irinsa ba. Daga nan kai tsaye part ɗin amaryar Kawu Imrana suka nufa. Ba wata babbar mace ba ce sosai, duka babban ɗanta shekararsa goma. Hakan ya sa suke shiri sosai da Maryama, ko gidan ta zo ma a ɗakinta take kwana. A falo suka zauna ita da wasu ƙawayenta da za su bi mota guda. Matar ta fito daga kitchen hannunta ɗauke da food flask ta ce, "Sannun ku. Kun gaji ba? Ai dole ne gajiya. Wannan uwar rawa da kuka sha. Ita kanta amaryar rawar da ta yi ai na sha mamaki." Ta ƙarisa da ajje food flask ɗin a bisa centre table. "Aunty Ruky ni kaina ban san yadda aka yi na dage rawar nan ba. Ni da rawa ma ba ta dame ni ba." Taɓe baki ta yi Aunty Ruky. Ta ce, "Ke gwara da kika yi. Komai na duniyar nan fa lokaci gare shi. Idan ba ki yi ba yanzu akwai sadda da kuɗi ma a ce ki yi ba za ki yi ba." Dariya suka ɗauka duka ƴan matan, suna kallonta. "Da gaske fa. Ku dai ku jira in fito ku sha labari." Ta koma Kitchen. Plates ta ɗauko sannan ta dawo, biye da ita ƴar yarinyar da ke mata aiki ce ta kwaso lemuka a babban tray. Bayan ta zauna ta ce musu, "Ku zuba abinci ku ci kafin ya dawo ɗaukarku. Na tabbata kuna jin yunwa, musamman ma ke amarya, na san amare abinci ba damun su ya yi ba." Da murmushi Maryama ta ce, "Za mu ci Aunty Ruky. Amma ki ba mu labarin da kika ce za ki ba mu." "To in faɗa muku lokacin aure na, ina ji ina gani kunya ta hana ni yin rawa. Kun san dai irin abun, mace ta auri wanda ba sa'anta ba, akwai jin nauyi sosai. Wallahi sai bayan biki na rinƙa da na sani. Har gobe ban daina ba. Har ji nake ina ma dai a dawo da bikin baya, ai da na yi rawa wadda wata ƴila har sai jikina ya ƙille, ke wata ƙila ma har sai Alhajin da kansa ya janye ni." Dariya suka sake ɗauka su duka. Dama haka take matar, akwai ta da wasa da dariya, ba dai a zauna da ita a yi ɓacin rai ba. Abincin suka ci kaɗan, sannan wayar Jiddah ta yi ƙara. Tana dubawa ta ga Deedah ne ke kiranta, ta ɗauka. Ce mata ya yi su fito ga shi nan ya zo, tana tsinke wayar ta faɗa musu. Aunty Ruky ta ce, "To kuma ko lemun ba ku sha ba. Aikam tafiya za ku yi da shi idan kun je gida ku sha." Suna faɗin ta bar shi ta bar shi amma ta ƙi, ta ce da mai aikinta ta kawo mata leda mai girma, ta juye musu duka lemukan, sannan ta sa ta kai musu har mota. Godiya suka mata sannan suka fita, sai famar dariya suke mata. Maryama na faɗin, "Ai ku ne baƙin Aunty Ruky. Haka take da ban-dariyar tsiya." Skwatin suka yi a motar ba ta amshe su ba, saboda yawan su, duk wanda za su kwana ne suke tare. Mutum biyu ma suka zauna a gaba; Jiddah da wata ƙawarsu Afrah. Bayan ya sauke su suka firfito, ya ce da Jiddah don Allah ta tsaya yana so su yi wata magana. Kallon Maryama da saudat da ke ɓoye dariyarsu ta yi, sannan ta musu gatsine da baki ta dawo ta tsaya kusa da murfin motar, shi kuma ya fito, ya zagayo inda take. Haka kawai kuma sai ya samu kanshi da rashin samun abun faɗi. Ɗan dafe kanshi ya yi, kafin ya ce, "Ba ku da buƙatar komai dai ko?" Da murmushi a fuskarta ta ce, "Babu komai Yah Deedah." "To shi kenan. Idan dai akwai abin da kuke so ko ma mene ne kina da numberna, kar ki samu damuwa kawai ki kira ni ko kuma ki min text." "To insha Allahu. Mun gode ƙwarai Allah saka da alkhairi." "Ameen ya Rabbi. Gobe dai na tabbata Dady da kanshi zai kai amarya gidanta. Motocin ɗaukar amarya za su zo, na yi magana da friends ɗina kamar yadda suka yi yau. Please kar ki hau motar kowa, saboda ina so mu yi magana ne bayan an kai amaryar. Ai babu takura ko?" "Ehh." Ta faɗa ƙasa-ƙasa cikin jin nauyinsa. "To ni bara na wuce Jiddah. Idan na koma gida insha Aahu I'll give you a call. Ki tabbatar kin saka ma cikinki wani abu." Kai kawai ta ɗaga mishi, sannan suka yi sallama ta shige ciki. Bai tayar da motarsa ba har sai da ya tabbatar ta shiga gidan. Tana shiga kuwa suka hau yi mata tsiya. Ba ta ce musu komai ba sai guntun tsakin da ta saki, sannan ta zauna bakin gado, tana jiran Afrah ta fito ta yi alwalla. Maryama kuwa suna shigowa ta ce musu za ta je ɗakin Abba, ba kuma can ɗin ta je ba, ɗakin Annur ta nufa cike da ɗokin ganinsa. Kwance ta same shi ya kalli can jikin bango, a tunaninta ma barci yake, saboda yadda ta ga ya takure wuri ɗaya. Gyaɗa kanta ta yi cike da tausayi, ta jawo blanket ta rufa masa, ta juya da nufin tafiya ta ji muryarsa ya ce, "Ni na yi fushi." Sassanyan murmushi mai haɗe da ajiyar zuciya ta saki, sannan ta juyo tana kallonshi. "Na'am me ka ce?" Ta faɗa a hankali. "Ba ke ce kika ƙi dawowa ba." "A yi min afwa. Kalla ka ga na kama kunnena, alamun na tuba kenan. Ba zan sake ba insha Allah." Tashi ya yi zaune yana kallonta, ya ɗan lumshe idanuwan kafin ya buɗe, ya ce, "Ai wannan mutumin ya zo nan, shi ya min wanka ma ya saka min wannan kayan masu kyau." Ya hau gwada mata light brown yadin jikinsa, wanda ya ji aikin hannu kalar coffee brown. Ɗaya daga cikin kayan da Kawu Imrana ya ɗinka masa ne. Kuma ɗazu da safe Uncle Marwan ya aiko masa da wasu kala biyu, cewa ya saka, duk da dai ba wurin ɗaurin auren zai halarta ba. "Inye angon nawan ba. Ka ga yadda ka yi kyau sosai kuwa? Tamkar na sace ka na gudu haka na ji." Harararta ya yi, ya ɓata fuska, ya ce, "Ai dai ba za ki iya sace ni ba. Yauwa, na tuno wani abu." Ya ɗora hannunshi a goshi alamar tunani. Ba ta ce masa komai ba, kamar yadda ta karanta, cewa ba a ma mutum gajen haƙuri a irin wannan lamurran, musamman ma masu matsalar ƙwaƙwalwa, ko kuma wanda ake tunanin sun samu lost of memory. Barin sa ake don kanshi ya faɗa. Ya yi kamar seconds arba'in a haka, kafin ya ce, "Wasu mutane ne suka kai ni gidansu, har suka cire min kayan jikina." Cike da mamaki ido a buɗe take kallon sa, ba kuma ta nemi jin ƙarin bayani daga gare shi ba, har sai da don kansa ya ce, "Kuma sai suka saka min wasu a jikina. Ni dai kawai na ce musu Amrah Nake So!" Ya saki dariya, yana mai bin ta da kallo. Ita ɗin ma dariyar ta ƙirƙiro, duk da cewa zancen nashi ya matuƙar ɗaure mata kai. Sosai take daɗa gode ma Allah. Domin kuwa ba laifi sauƙi na zuwa, addu'arta tana amsuwa. Kuma sannan tana saka shi shi ma yana ma kanshi, tana faɗi yana faɗi. Ga Muhammad ma ƙaramin yaro, duk sadda zai yi sallah to sai ya saka Annur a addu'arsa. "Ka ci abinci dai ko?" "Hammad ɗan yaron nan ya kawo min, kuma ya zauna har sai da na gama ci na sha magani, sannan ya tafi." Ya kama lila kanshi, yana dariya. "To masha Allah! Haka nake son ji dama. Bari in je in samu ko wanka in yi, ga sallah ban yi ba. Gidan akwai mutane sosai, baƙi wanda suka zo biki. Ba za ka gan ni ba sai gobe. Goben ma ba sosai za ka samu gani na ba. Ai za ka yi haƙuri ko?" "Ehh mana. Ba kin ce aure za a ɗaura mana ba?" Mamaki take sosai, ashe dai bai manta ba. Ta ce, "Haka ne kuwa Yah Noor ɗina. Bari in tafi to. Sai da safe." Kansa ya ɗaga mata, sannan ya koma ya kwanta. Sai da ta kashe masa wutar ɗakin sannan ta fice zuwa nata ɗakin. * Washe gari Jumu'a, tun da sassafe Maryama ta yi wanka, ta shirya cikin atamfarta Julios Holland wadda ta ji ɗinkin riga da zani half gown. Ɗaurin ɗankwalin Zahra Buhari da ake yayi ta cancaɗa, ta feshe jikinta da turaren Cinema, sannan ta yafa gyale madaidaici. Kyau iya kyau ta yi shi, duk da cewa ba wani make up ta yi sosai ba. Sai da ta gama duka sannan ta ce da su Jiddah tana zuwa. Ko ba ta faɗa ma Jiddah ba ta san inda za ta je. Hakan ya sa kawai ta sakar mata tattausan murmushi, sannan ta fice daga ɗakin. A hanyarta ta yi kiciɓus da Umman Amrah. Aikuwa cikin fara'a sosai ta rungume ta, tana faɗin, "Umma baccin ƴa ba ta isa ta yi fushi da Ummanta ba, nikam dai da na yi da ke." Ta ɗan ɓata fuskarta alamun shagwaɓa. Umma ta ce, "Yi haƙuri ƴata. Wallahi abubuwa da yawa ne suka hana ni sake dawowa. Na farko dai kin ga Mallam ya sha ciwo kwanakin nan, wanda ko kaɗan kin ga bai kamata na fita ba. Na biyu kuma sai na yi baƙuwa, ƙanwata ta zo daga Kano musamman gidana ta sauka. Kin ga ai bai kamata na fita na bar ta ba." Murmushi Maryama ta saki, ta ce, "Allah sarki! To ya jikin Mallam ɗin yanzu?" "Jiki da sauƙi sosai Maryama. Ya warware ma har ya koma wurin aikinsa. Sai jiya ai na ga saƙonki na waya. Cewa yau Jumua za a ɗaura miki aure da Annur. Da yake wayar na jefar kin san halina, ban kuma waiwayarta ba sai jiya, ina buɗewa na ci karo da saƙon. Wallahi inda na sani da da ni za a yi komai. Rashin sani ne." "Babu komai ai Umma. Mu je na raka ki wurin Mama." "Ai har na zauna a falo kuma dai na ga babu wanda na sani. Na kusa minti talatin fa a zaune." "Eyyah! Ai ban sani ba wallahi. Kin san gidan taro ya gaji haka. Kuma ban ma san cewa Mamar ba ta fito ba. Mu je ko?" Suka nufi ɗakin Mama. Tun daga bakin ƙofa mutane ke ta famar tsokanar Maryama suna faɗin ga amarya ga amarya, wasu sai waƙar tsokana suke mata. Murmushi kawai take sakar musu har suka ƙarisa gaban Mama. Da faraa Mama ta yi ma Umma marhabun da zuwa. Sannan ta gyara mata wurin zama ta zauna. Sai da Maryama ta tabbatar da Umma ta samu wurin zama sannan ta bar ɗakin, ta nufi ɗakin Annur. Wata irin dakakkiyar farar shadda ce a jikinsa, wacce ta ji surfani kalar light blue. Fuskar nan tasa ta yi sayau, saboda sabon askin da mai gadi ya masa, har da gyaran fuska. A gefensa ta zauna, tana ƙare mishi kallo, shi ɗin ma yana bin ta da kallo. Kafin ta ce mishi komai ta ji ya ce, "Kin yi kyau." Ya langaɓe kanshi yana murmushi. "Kai ma haka." Ta faɗa tana mai juya zoben hannunta. Sai da ta ɗan sassauta muryarta sannan ta ce, "Jiya kana ta juya zoben nan sannan ka dawo da shi ka saka min. Akwai damuwa ne?" Shiru ya yi jim! Kafin ya ce, "A ina kika same shi?"" Ta ji ya faɗa, yana miyar da dukkanin hankalinsa gare ta. Ɗan jujjuya zoben ta yi sannan ta zaro shi daga yatsar tata. Ta miƙa masa ya karɓa ya riƙe shi. "Kalli da kyau Yah Noor. What can you remember about it?" Shiru ya mata, bai daina jujjuya zoben ba, bai kuma miyar mata da shi ba. Sai da ta gaji da shirun don kanta, sannan ta ce, "Uncle Marwan ɗin nan da na faɗa maka, shi ya haɗo min da shi a cikin lefena." Zumbur Annur ya miƙe tsaye. Idanuwansa suka gama firfitowa, ya ce, "Ba naki ba ne! Wallahi ba naki ba ne ba, na Amrah ne!" Miƙewar ita ma ta yi, idanuwanta suka cicciko, ta ma rasa abin da za ta faɗa. Ba ta san me ya sa ba, a yanzu ta fara jin kishin Amrah. Ita kanta tana mamaki, ta yadda lokaci guda ta fara kishi da matatta wacce ba ta raye. Amma kuma me zai sa ya dame ta da xzncen Amrah, bayan kuma ita zai aura? Kenan ma zoben yana da wani asali, da ba ta gama sani ba? Fizge zoben ta yi daga hannunshi, ya bi ta da kallon mamaki. Cikin drowar da magungunansa suke ta jawo ta ciri wata takarda daga jikin jotter. Ta nannaɗe zoben a ciki sannan ta jefa dunƙulen takardar cikin drowar, ta rufe. Dawowa ta yi a gabanshi, ta rusuna har ƙasa, tana hawaye ta ce, "Da alama dai zoben nan asalinsa ba nawa ba ne ba, duk da dai ban gama gasgatawa ba. Amma dai ga shi nan, na miyar maka a inda karikitanka suke. Duk ranar da ka dawo cikin hankalinka, ka ba ni kyautarsa da hannunka, to zan karɓa. Amma for now, bai zama haƙƙina ba." Ta miƙe haɗe da ficewa daga ɗakin. Sai da ta ja ƙofar ta rufe, sannan ta ƙarisa isa part ɗin Abbansu. Ta samu daidai Abban nata zai fito shi da Kawu Imrana. Har ƙasa ta duƙa ta gaishe su, kawu Imrana ya ce, "Amarya kin sha ƙamshi. Sai wani haske kike ba ki gan ki ba." Murmushi ta saki kanta a sunkuye tana jin kunya sosai. Kawu ya ce, "Akwai abin da kike buƙata ne?" Ba ta ɗago kanta ba ta ce, "Dama muna son key ɗin ɗakin Abba ne, ɗakina ba zai ɗauki ƙawayena duka ba." Cire mukullan ɗakin nashi ya yi daga jikin na motarshi, sannan ya miƙa mata, yana faɗin, "A kula sosai don Allah. Ko ki rufe min bedroom, tunda dai falon da girma." "To Abba insha Allah." Ta faɗa bayan ta miƙe tsaye, ta basu hanya suka wuce ita kuma ta koma ɗakinta domin tahowa da ƙawayen nata. * Ƙarfe uku daidai na rana al'umma da yawa suka shaida ɗaurin auren Annur da Maryama, wanda Uncle Marwan ya zama wakilin ango, kawu Imrana kuma waliyyin amarya. * Dafe zuciyarsa ya yi sanadiyyar sauya salon bugawa da ya ji ta yi. Cikin ƙanƙanin lokaci ya rinƙa jin wani irin sanyi na ratsa duk wata tsoka da ke cikin zuciyarsa. Samun kansa ya yi da murmusawa, yana jin yadda ƙamshin turaren da ke jikinsa ke rikeɗewa izuwa ƙamshin turaren Maryama da ta bar ɗakin tun kusan awanni biyar da suka shuɗe. * Guɗar da suka jiyo ana rangaɗawa ne ya basu tabbacin an ɗaura. Nan fa ƙawaye suka fara faɗin, "Amarsu ta ango! An daura..." Ba ta san sadda ta fashe da kuka ba. Ta duƙar da kanta bisa cinyarta, tana zubda ruwan hawaye. Jin abun take tamkar a mafarki, wai yau ita ce ta zama matar Annur, matarsa ta sunnah. A wani ɓangaren kuwa tausayin kanta take; ta auri mutumin da bai kasance mai hankali ba. Wanda ta tabbatar da duk sadda ya dawo cikin hankalinsa ba lallai ba ne ya iya ci gaba da rayuwa da ita. Me ya sa zuciyarta za ta mata haka? "Amarya na kukan murna. Mun san komai yarinya, gwara ma kawai ki yi shiru ki daina yin shi." Ba ta ko kula su ba ta ci gaba da kukanta. Ganin haka ya sa kuma suka hau rarrashinta. Jiddah ta dafa bayanta sai famar ba ta haƙuri take, har suka samu ta yi shiru. Miƙewa ta yi a bisa ƙafafunta, cikin rashin kuzari ta fara takawa, duk irin taron mutanen da ke wurin a haka ta rinƙa kukkutsawa har ta isa ɗakin Annur. Tana zuwa ta gan shi zaune, ba ta san sadda ta rungume shi ba. Tsam-tsam ta masa tamkar wani zai ƙwace mata shi. A tare bugun zuciyarsu ya rinƙa tafiya, suna jin yadda ni'ima ke sauka a cikin duniyarsu. Cikin muryar kuka Maryama ta ce, "An ɗaura Yah Noor! Shi kenan na zama mallakinka, ka zama nawa. Rayuwarmu ta dawo a ƙarƙashin inuwa guda. Ina ƙaunarka Yah Noor, da dukkanin zuciyata. Daga farko na ɗauka ko tausayinka kawai nake, a zato na taimakon ka ne nake da muradin yi. Sai a yanzu nake daɗa tabbatar da ƙaunarka nake, ƙauna mai tsananin gaske. Don Allah ka min alƙawari, cewa ba za ka taɓa rabuwa da ni ba, duk wuya duk rintsi. Don Allah ka ba ni fili a cikin zuciyarka, ni ma in gwada kwance tawa hajar a cikinta. Na ɗauki alwashin zame maka Amrarka, na maka alƙawarin ba ka duk wani gata wanda ya kamata mace ta bai wa mijinta. Zan kasance mai alfahari da kai, duk tsanani duk jin daɗi." Ta janye jikinta daga nashi, tana faɗin, "Say something please. Ni ma ka ce da ni kana so na. Na zama halaliyarka Yah Noor." Murmushi kawai yake sakar mata, ya gagara furta komai. "Tunda ba za ka faɗi komai ba ni zan tafi. Ina da baƙi sosai. Amma please idan na ce wani abu kai ma ka maimaita. Ka ji?" Ɗaga mata kai ya yi, yana kallonta. "Allah ya ba ni lafiya" Ya maimaita shi ma a hankali. "Ya warware min dukkanin damuwata." Bayan ya faɗa har sau uku sannan ta tafi, ta jawo masa ƙofar ɗakin, tana yi tana waige. Sai zolayarta ake har ta samu ta isa ɗakin Abba. Dr. Islam ta samu zaune kan stool, tana latsa wayarta. Isa ta yi inda take, ta rungume ta da murna, tana faɗin "Aunty Islam ashe kin zo." "Na zo Maryam. Kin je ina ne?" "Na zagaya baya ne. Kun zo lafiya? Ina Abdul ɗina da kuma Momyna?" "Abdul na can sun haɗe da Hammad tun muna shigowa, daidai su kuma sun dawo daga wurin ɗaurin aure. Momy kuma tare muka shiga ɗakin Mama, ta ga Mahaifiyar wata yarinya da ta rasu ne, Amrah. To suna abun arziƙi ta zauna inda take suna fira." Dariyar yaƙe ta yi Maryama. Tana gudun kar Umman Amrah ta kwafsa, kodayake dai ta san komai, ta san cewa basa son dangin Annur ɗin su sani yanzu. Ƙarfe biyar na yamma motocin ɗaukar amarya suka hallara a ƙofar gidan su Maryama. Nan fa mutane suka isa gaban motocin, aka hau shiga. Maryama kuwa ta canza kaya, ta saka wani jan material da aka ma ɗinkin doguwar riga, ta saka alkyabba kalar golden. Yayar Mama mai suna Goggo Rabi da Umman Amrah ne suka taho da Maryama, bayan ta samu nasihu sosai daga mahaifiyarta da kuma danginta. Kuka sosai take yi, har suka iso gaban motar kawu Imrana, saboda dama ita kawai yake jira tun ɗazu. Ƙawarta Saudat ce ta zauna a gaban motar Kawu Imrana ɗin, sai amarya da iyaye a baya, tana tsakiyarsu. Jan motar ya yi kawu, a hankali sautin kukan Maryama ke fita, wanda tun ɗazu take yin sa. *** *To mutanena. An ɗaura fa. Are you happy? Na san kun ji daɗi, confirm. To sai a ba ni ladar aikina🤒.* *Maryama dai ta auri mahaukaci Annur. Ko ya zaman nasu zai kasance? Wannan zoben na zinare da suka yi maganarsa, me yake ƙunshe da shi? Amsoshin suna gaba, insha Allah.* *Don Allah ku taimaka min gobe kar wacce ta nemi ANS, ni ma in huta haka nan.* Thanks all. Pinky durling💞 RAZ 2 [9/17, 1:27 AM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taɓa zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 6⃣5⃣ Wattpad: PrincessAmrah *** Hangame gate ɗin gidan aka yi, Kawu Imrana ya shiga har cikin gidan da motarshi. Bayan ya gyara parking ne iyayen suka fito da Maryama da har yanzu ke ta famar cizgar kuka. Sadda suka isa bakin ƙofar shiga part ɗin nasu, sai da ta karanta addu'o'i sosai kafin ta ɗora ƙafarta a bisa ƙofar ta shige ciki. Sauran ƴan ɗaukar amarya kuwa sai da aka sha zagaye da su sosai, kusan duk girman Katsina sai da suka zagaye shi. Ring roads ɗin nan kaf sun ga bayansa, kafin suka ƙarisa isowa gidan amaryar. A lokacin har magrib ta bada baya, gari ya fara yin duhu. Daga can nesa kaɗan da gidan Deedah ya faka motarshi, rage ƙarfin AC ɗin ya yi, yayin da ya juyo ya fuskanci Jiddah da dukkanin hankali da nutsuwarsa. Kanta ta sunkuyar ƙasa, tana bin zanen lallen hannunta na hagu da yatsunta na hannun dama, tana sauraren abin da zai fito daga bakinsa. Ajiyar zuciya ya sauke, yana bin ta da kallo, kafin ya saita kansa, ya ce, "Jiddah..." Ya dakata daga nan, jin yadda sunan nata ke neman yi masa nauyi a bakinsa. "Na'am." Ta faɗa haɗe da ɗan ɗago kanta ta kalle shi, sai kuma ta samu kanta da ƙoƙarin rasa nutsuwarta, haɗa idanuwan da suka yi a lokaci guda. "Jiddah ina neman wata alfarma daga gare ki." "Am all ears Yah Deedah." "Jiddah please, will you marry me?" Duk da cewa ta karanci yadda soyayyarta ke ɗawainiya da shi duk a cikin kwanakin nan. A ɗan haɗa idanuwan da ta yi da shi cikin seconds kaɗan, ta ga zallar soyayyarta a cikin idanuwansa. Amma bai hana ta mamakin jin kalaman nasa ba. Sai ta rasa abin da za ta faɗa, kawai ta masa shiru. "Don't say no Jiddah. Wallahi I love you with all my heart. Don Allah kar ki watsa min ƙasa a ido. Kin ga Maryam ta ƙi ni, kar ki min irin nata. Please." Baki ɗaya ya gama marairaice fuska tamkar ba shi ba. Ita kanta mamakin yadda ta ji yana ƙanƙan da murya take. "Yah Deedah..." Ya gaggauta kasa kunnuwansa domin jin kalaman da za su fito daga bakinta. "Akwai wanda nake tare da shi, tun kusan shekara biyu muke tare. To matsalar da aka samu, tun tsawon watanni biyar zuwa shida da suka shuɗe, Abbana ke bin kansa da ya turo, amma ya ƙi turowa. Ni kaina na kasa fahimtar inda ya dosa. Sannan kuma kullum idan muka yi waya da shi sai famar cika ni yake da daɗin baki. Ina ƙaunarsa duk da hakan Yah Deedah." Idanuwanta suka yi rau-rau tamkar za ta yi kuka. "To ya isa Jiddah. Ni dama ban isa na miki dole ba. Yadda duk kike so haka za a yi." Yana jin yadda kishi ke masa tuƙuƙi a cikin zuciyarsa. Har ji yake inda ma a ce wancan saurayin nata yana a gabansa, zai iya faffalla masa mari zafafa kala biyar. Sai dai kuma me, a kodayaushe ƙoƙari yake na ganin ya rangwanta ma kansa wannan zazzafan kishin da ke gare shi. So yake ya ga ya rangwanta wa zuciyarsa, ya rinƙa kai ta nesa a duk sadda kishinsa ya motsa. Shiru ne ya biyo baya a motar, kafin Jiddah ta yi ƙarfin halin faɗin, "Sai dai kuma son nashi a banza ne, tunda shi ya ƙoƙarta ƙaryata kansa na faɗar da yake yana so na. Duk wani namiji matuƙar yana son mace tsakaninsa da Allah, to daɗi zai ji idan aka ce masa ya turo iyayensa a yi maganar aure. Ba wai halin yin auren ba ne Tahir ba shi da shi, na samu raɗe-raɗi ne cewa akwai wacce ake so a aura masa a gidansu, duk da dai shi ya ƙaryata min hakan. Yah Deedah..." Ta sassauta muryarta tana kallon shi. "If you are ready to marry me, then I'm ready too to accept you as my fiancee." Kansa da ke jingine da sitiyari ya ɗago da mamaki yana kallon ta. Karkaɗe kunnuwansa yake kamar dai ba daidai ya ji zancen ba. A tunaninsa ko don yana son ta amince ɗin ne ya sa kunnuwansa suke masa wannan gizon. Ganin haka ya sa Jiddah murmusawa, ta ce, "Na amince Yah Deedah. Na amince zan aure ka, da dukkan zuciyata." Sassanyan murmushin da ke daɗa ƙawata fuskarsa ya saki. Bai san sadda ya furta 'Alhamdulillah!' ba. Sannan ya ce, "Na matuƙar jin daɗin kalamanki Jiddah. And I promise to make you happy, till the end of my breath. Ina ƙaunarki Jiddah. Ina matuƙar son ki." Tattausan murmushi ta sakar masa ita ma. Ta ce, "I know, Yah Deedah. I can see it in your eyes." Jinjina mata kansa ya yi, kafin ya ce, "Na samu abin da nake so, sai ki shiga ciki ko? Duhu ya fara, ga shi ba ki koma ba. Ba na so zargi ya shigo ciki." "Haka ne." Ta faɗa kanta a sunkuye, sai kuma ta samu kanta da jin kunyarsa. Wayarta ce ta ɗauki ƙara, tana dubawa ta ga sunan Hadiza a bayyane. Ɗaukar kiran ta yi haɗe da karawa a kunnenta. "Na shigo cikin GRA ɗin Jiddah. Ta ina zan yo kuma?" "Kina daidai ina yanzu?" Jiddah ta tambaye ta. Alama Deedah ya mata kan ta dakatar da ita, sai su je su zo da ita kawai. Abin da ya faru ɗin kenan. Ta ce mata tana daidai round about na GRA. A nan ta ce ta tsaya ta jira su, za su zo su ɗauke ta. A can ɗin kuwa suka same ta zaune kan wata kujerar ƙasa, irin wadda ake ajjewa kusa da manyan rounds. Tana ganinsu ta taso ta yo inda suke. Bayan motar ta buɗe ta shiga, tana faɗin, "Sannunku." Jiddah ta ce, "Yauwa. Hadiza masu zuwa biki da dare." Ta dafe kanta. "A yi haƙuri. Kin san na koma Maraɗi ne, shi ya sa ma da kika ce za ku kawo min IV na ce muku bana nan. Na koma gida ne, a gaban iyayena. Tun da safe na so in taso kuma, sai kuma muna wani bikin ne, ƙanwar mijin yayata ake ma aure, yayar tawa ta ce ban isa in taho da wuri ba, sai dai in bari har da yamma sannan in taho sai in kwana a nan ɗin." Jiddah ta murmusa, ta ce "Sannu to ai mun gode da hakan ma." "Angon naki ne wannan? Na ga kun yi matching sosai." Kallon juna suka yi Jiddah da Deedah. Deedah ya ce mata, "Namu za ki zo next insha Allah." Kunya sosai Jiddah ta ji, ta masa hararar wasa. Bayan sun isa gidan amaryar, sai da Hadiza ta fita sannan suka yi bankwana, Deedah na ce mata duk matsakar da gare su kar ta ji komai kawai ta kira shi, insha Allahu zai musu koma meye. Tare suka shiga cikin gidan, Jiddah da Hadiza. A lokacin duk an gama watsewa, wanda za su kwana kawai suka rage, sai kuma Dr. Islam da mutanenta; Hammad da Abdul-Ahad. * Sosai suke nishaɗi a gidan amaryar, kusan ƴan mata takwas ne za su kwana, babu iyaye a cikinsu duka iyayen sun gama tafiya. Sai famar tsokanar Maryama suke, murmushi kawai take sakar musu, a wani ɓare na zuciyarta kuma ba ta daina al'ajabin zoben nan ba. Haka kawai take jin faɗuwar gaba tunda al'amarin zoben ya kasance. Ta rasa dalili. Gama sallarta kenan Jiddah ta ninke hijabin ta miƙo ma Maryama. "Oya take your hijab. Kar sai bayan biki ba ki ga wannan hijabin naki na gado ba ki ƙwala min kira a waya." Murmushi kawai ta saki, ba tare da ta furta komai ba. Saboda ita kam yadda jikinta ya gama saɓulewa, ko yawaita surutu ma ba za ta iya yi ba. "Wannan Jiddar tunda suka iso sai wata fara'a take da na kasa fahimtar dalilinta." Saudat ce ta yi wannan maganar, tana latsar waya tamkar ba ita ce ta yi maganar ba. Caraf Hadiza ta ce, "Ah to ba dole ku gan ta a cikin nishaɗi ba." Ɗago kai Saudat ta yi tana murmushi, ta ce ma Hadiza "Gist me ƙawata. Wani abu ya faru ne?" Hadiza ta saki murmushi tana kallon Jiddah, ta ce, "In faɗa ko kar in faɗa?" Banza ta mata, tana sakin guntun murmushi. "Tunda ba za ki yi magana ba to bara kawai in tona. Tare take da Habibin nata fa, su suka ma ɗauko ni da kansu. Wannan ango nata ko tsageran ango. Baida kunya ko ɗiris." Duka ɗakin suka kwashe da dariya, har da Maryama. "Hadiza sharri ko?" "Ba wani sharri Jiddah. Ai wani mayen kallo da na ga yana miki na jima ina mamaki. Har da kunyata ba ku ji ba." Dukan wasa Jiddah ta kai mata. Ta ce, "Kina nufin muna gaba kina baya amma har kin hangi muna wani irin kallo? Hadiza fear God wallahi." "To na ji. Amma dai wace irin soyayya ce ba ku yi a gabana ba? Malama ni fa har sai da na ji ina ma a ce ba mu iso ba. Saboda ina kallon ku ina ƙara koyon soyayya." Sosai suke dariya. Suna matuƙar jin daɗin hirar tasu. Har dare ya nisa amma ba su sani ba. Dama tun wuraren takwas Kawu Marwan ya aiko musu da take away na chips da kaji da yawa yadda zai wadace su. Cikin muryarta da ta gama disashewa da kuka ta ce, "Wai ni kam Hadiza ina Fiddou ne?" "Fiddou ta yi aure Maryam." Cikin mamaki Maryama da Jiddah suka kalle ta. "Ta yi aure? Yaushe? Wa ta aura?" Duka a jere Maryama ta yo ma Hadiza wannan tambayoyin. "Yau ɗin nan aka ɗaura mata aure. Ai shi ya sa ma ban zo da wuri ba. Aunty Sahiya ta ce bai kamata in taho tun safe ba tare da na tsaya har a ɗaura aure ba. Ta auri wani Mahmouda. Yauwa, ƙila ma za ku san shi. Ta ce min wai shi ne wanda ya taɓa kaɗe Modu da mota." Murmushi Maryama ta saki, wanda yake kai tsaye tun daga cikin zuciyarta. Da biyu ta yi murmushin. Na farko ta jiye ma Fiddou daɗi da ta yi aure. Na biyu kuma ko ba komai ta huta da alƙawarin da ta ɗaukar mata, kan cewa Annur da kanshi zai koma ya aure ta. "Amma kuwa na ji mata daɗi sosai wallahi. Allah ya sa alkhairi ya ba su zuria ta gari." "Ameen Jiddah. Daga nan kuma sai ina? Sai gidanki." Ta yi dariya. Haka dai suka ci gaba da hira sosai har kusan uku na dare sannan suka yi barci. Da asubar fari kuma ɗaya daga cikin ƙawayen amarya mai suna Humaira ta tashe su. Sai masifa suke mata amma ta hau yi musu dariya, wai ai dama gidan amarya ba wani barci ake yi sosai ba. Hakan dai suka daure duk suka miƙe, suka jira lokacin sallah ya yi sannan suka gabatar. * Ba wani abu aka yi ba washe gari asabar. Kawai dai sauran tarkacen amarya da ba a kawo ba ne aka ƙarisa kawo su. Ƴan matan suka jejjera mata, sannan duk wani jere da manyan suka yi ranar jere da suka ga kamar bai yi ba, suka bi duk suka gyaggyara shi. Gidan su Maryamar ne aka yi guntun taro, shi ɗin ma don kar a ce ba a je gidan amarya an yi wani abu ba ne. Da yamma suka fara warwatsewa har Hadiza ma ta tafi, ya rage daga Jiddah, Saudat sai Afrah kawai suka yi saura. Share mata ko'ina suka yi suka mata goge-goge. Toilets duk inda aka ɓata suka bi suka goge shi. Misalin tara na dare motar da za ta ɗauke su ta zo, wadda Deedah ya turo kawai don ya musu wayo ya samu su tafi ko zai samu shan hira da masoyiyarsa. Hakan kuma sai ya ma Jidda da Maryana daɗi, koba komai za a kawo ango ba a gaban su Afrah ba, tunda ba su san komai game da shi ba. Ƙarfe tara da rabi Abba, kawu Imrana da kuma Uncle Marwan suka iso gidan, tare suke da Annur da ya sha wankan wani dakakken yadi kalar ruwan madara, an ƙawata ɗinkin da surfani shi ma irin kalar, ga hula kalar kayansa wadda ta yi matching sosai. Fuskar nan tasa mai cike da walwala ta yi fayau, sai famar sakin dariyar yaƙe yake, wacce in ba ita ɗin ya yi ba, babu wanda zai kalle shi ya ce mahaukaci ne. A rufe falon yake, suna ciki su biyun Maryama da Jiddah suna hira, Jiddah na daɗa ƙarfafa mata guiwa a kan rayuwar aurenta. Tana mata nasiha cikin hikima kan yadda za ta zauna da mijinta, duk da kasantuwarsa mara hankali. A ƙarshe ta ce mata, "Maryam ahir ɗinki da fitar da sirrikan aurenki. Kin ga dai mafi kusanci a cikin ƙawayenki da ke ni ce ko?" Maryama ta ɗaga mata kai. "To ko ni kar ki taɓa yin kuskuren faɗa min rayuwarki ta aure. Shi sirri sirri ne. Wannan al'amarin a tsakaninki da mai gidanki ne kawai. Duk wata ƙawa da za ta buƙaci sanin wani abu game da auratayyarki, ki kwaɗa mata maganar da ba za ta sake gigin tambayarki ba." "To insha Allahu zan kula sosai." Kafin su sake cewa komai suka ji knocking. Hakan ya tabbatar musu da cewa Annur ne aka kawo, tunda dama kawu Imrana tun ɗazu ya kira Maryama, cewa da kanshi zai kawo ango. Da sauri Jiddah ta yafa mayafinta sannan ta isa falo ta buɗe ƙofar. Murmushi ta saki tana mai buɗe musu hanya su wuce. Sosai ta yi mamakin yadda Annur ɗin ya ɗau wanka, ya sha kyau sosai. Har ƙasa ta gaishe su, kafin Kawu Imrana ya ce da ita ta shiga ta kira Maryamar. Tare suka fito, fuskar Maryama lulluɓe da tafkeken gyale, Jiddah ta daho ta har suka ƙariso falon. Daga ƙasan Kawu Imrana suka zauna su biyun, tare da miyar da hankulansu ga iyayen nasu. Uncle Marwan ne ya fara da faɗin, "Zan fara da godiya ga Allah maɗaukakin sarki, da Ya nuna mana wannan gagarumar rana, mai albarka a gare mu baki ɗaya. Haƙiƙanin gaskiya ba ni da bakin da zan iya yi miki magana Maryam. Domin kuwa kin gama mana komai, kin yi jihadi mai girma na zaɓen Annur a matsayin mijin aurenki na din-din-din. Allah Ya saka miki da alkhairi. Allah ya baku zaman lafiya ya kuma ba Annur ɗin lafiya." Ya juya da faraa ya fuskanci kawu Imrana, ya ce, "Alhaji Imrana na gode ƙwarai da wanann halacci ko in ce jihadi naku. Haƙiƙanin gaskiya samun dattijawan kirki kamar ku sai an tona. Kuka aurar da ƴarku mai cikakkiyar lafiya ga Annur da ya kasance ba mai hankali ba. Allah ne kawai zai iya saka muku. Na gode ƙwarai, Allah ya bar zumunci." Murmushin dattako suke saki su duka ukun, kawu ya ce, "Ai wannan tamkar yi wa kai ne. Fatar mu dai kawai Allah ya ba su zaman lafiya. Shi kuma wancan ɗin Allah ya toni asirinsa. Insha Allahu Annur zai samu lafiya, da kansa zai koma gidansu gaban iyayensa." Abba ya ce, "Allah ya yarje mana." Ya dubi Maryama da ta sunkuyar da kanta cikin gyale tana ta famar kuka ya ce, "Maryam na san mun ba ki tarbiyyar kirki, tun yarintarki har kika girma. Ina so ki yi amfani da iliminki na addini da kuma na zamani, ki bi mijinki sau da ƙafa, ki masa biyayya, kar ki dubi cewa wai mai laruri ne, babu ruwan Allah wallahi. Matuƙar kika saɓa ma mijinki to tsaf za a rubuta miki zunubi. Duk da yake a haka, to Aljannarki a ƙarƙashin tafin ƙafarsa take. Ki kiyaye, ki ba shi dukkanin kulawa tamkar yadda za ki ba mai cikakkiyar lafiya. A ƙarshe, sai in ce na yafe miki duniya da lahira. Allah ya miki albarka ya ba ki zaman lafiya da mijinki. Kar a fallasa sirrin aure Maryam. A kiyaye." Kuka take yi sosai, tana jin yadda ƙaunar mutanen ke daɗa shiga cikin zuciyarta. Har ma dai Abbanta, da duk zafin da ya ɗauka da ita ya sauke shi. "To mu bari mu tashi mu tafi. Ƙawar amarya a nan za ki kwana ne?" Cikin zolaya kawu Imrana ya yi wannan tambayar yana kallon Jiddah. "A'a kawu. Yanzu ni ma nake son tafiya." "Ah to madalla. Sai mu tafi tare ai mu sauke ki." Dariyar yaƙe ta yi, tuna cewa Deedah ya ce zai zo ya kai ta gida da kanshi, har ma ya shiga ya gaishe da ƴan gidansu. Kama Maryamar ta yi suka nufi ɗaki. Uncle Marwan kuma ya kalli Annur da tun ɗazu yake ta wasa da kafet ɗin ɗakin yana bin zanensa. "Annur! Duk da na san cewa ba ka kasance mai lafiya ba, amma hakan ba zai hana ni yi maka nasiha a matsayina na maɗaurin aurenka ba. Ka kula sosai, don Allah ka yi haƙuri da matarka, duk wuya duk runtsi kar ka taɓa butulce mata, ka ga dai yadda ta sadaukar da rayuwarta a kanka, ba tun yanzu ba. Ka riƙi Maryam da amana, ka tsaya tsayin-daka wurin ba ta farin ciki, tun daga yanzu har zuwa sadda za ka dawo cikin hankalinka. Na tabbata hankalin Maryama ba za ta taɓa barin ka ka wulaƙanta ba." Tamkar yana magana da gunki haka ya yi. Sai dai ci gaba da wasanshi kawai da ya yi, yana sakin murmushi. Amma fa bai ɗago ya kalle shi ba. Fitowar Jiddah ya sa duk suka miƙe, a lokacin har text ta gaggauta yi ma Deedah, cewa Abbanshi ya ce da kansu za su miyar da ita gida. "Ta shi ka bi ta ta kai ka ɗaki." Uncle Marwan ya faɗa, yana kallon Annur. Babu musu kuwa ya miƙe, ya bi bayan Jiddah da ta masa jagoranci har zuwa ɗakin. Tana fitowa suka fice, dama Uncle Marwan ya kawo musu ɗaya daga cikin masu gadin gidanshi, tunda ya san cewa dole suna da buƙatar mai kula, kasantuwar ba wani tsayayyen namiji a gidan. Bayan sun fita mai gadi ya rufe gidan, yana ɗaga musu hannu. *** *Kun ga unexpected post ko? Ko ni ban tsammaci za ku same shi ba gaskiya. Kuma ba laifi ya yi tsawo, har ma ya zarce ma tunanina. Idan kun ji daɗinsa, please and please pray for me; Allah ya biya min dukkanin buƙatuna na alkhairi, da sauran ƴan uwa musulmai.* *Dan-dan-dan-dan-dan-dan!😀 Ga amarya Maryama ga kuma angonta Annur. Ko ya wannan rayuwar aure za ta kasance?* *Mu je zuwa dai.* *Ina daɗa gaishe ku masu mutunci. Ku ci gaba da aikinku, ladar ku na a hannuna, zan ba ku ita ta hanyar ci gaba da kawo muku zura-zuran pages...lol.* Thanks all. Pinky durling💞 RAZ 2 [9/18, 4:14 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 6⃣6⃣ Wattpad: PrincessAmrah *** Ji ta yi an dafa ta, hakan ya sa ta dakata daga kukan da take yi, ta ɗago kanta tana kallon yadda ya yaƙe bakinsa yana mata dariya. Tozalin da ya yi da rinannun idanuwanta da ke zubar da ƙwalla ya sa shi dakatawa da dariyar, tamkar bai taɓa yin murmushi ba. "Me aka miki? Ko ni ne?" Ƙirƙiro murmushi ta yi tana kallon shi cikin ido, ta ce, "Ba kai ba ne Yah Noor, tsakuwa ce ta faɗa min a cikin idanuwan." Gyaɗa mata kai ya yi, sannan ya ce, "Ki yi haƙuri kin ji. Za ki warke insha Allahu." Sassanyar murmushi ta saki, ta ce "Allah ya yarje mana. Yanzu ka samu ka yi wanka, ga kayanka can a cikin wardrob da Mama ta aiko da su ɗazu, sai ka sauya na jikinka." Kallon ta kawai yake a tsayen da yake, bai san yadda zai yi ya yi wankan ba. Mallam Mai gadi ne ke masa dama ko a gida. Kallon da yake mata ya sa ta gano manufarsa, cewa ba zai iya ba. Ta ce, "Ba za ka iya yi ba? Well. Bari in ɗauko maka da koda jallabiya ce sai ka canza. Amma ai ba za ka kwana da wannan kayan ba, ba ma za ka taɓa jin daɗin barcin ba." Ta miƙe tsaye. Tafkeken gyalen da ke jikinta ta ɗora a bakin gadon, ta gyara zaman rigarta, sannan ta isa bakin wardrobe ɗin. Wata jallabiya ce ta ɗauko masa kalar coffee brown. Bayan ta rufe wardrobe ɗin ta dawo kusa da shi, ta ajje kusa da inda ta ajje gyalenta, sannan ta ce masa, "Ina zuwa." Ta fice daga ɗakin, ta nufi nata. Cikin kayanta ta duba ta ɗauko wata rigar barci mai ɗan tsawo, za ta wuce guiwa. Sauya na jikinta ta yi da rigar barcin, sannan ta sako hula mara nauyi, ta zumbulo hijabi har ƙasa ta dawo inda yake. Kamar wasa ta tarar har ya cire na jikinsa ya saka jallabiyar, ya yi tsaye ƙerere gaban madubi yana kallon kanshi. Mamaki ta yi sosai, sai kuma ta saki murmushi, ta ƙarisa gabanshi tana faɗin, "Inye, angon ba. Har ka canza kenan. Ka ga yadda ka yi kyau kuwa? Yanzu ka san me ya rage?" Ya gyaɗa mata kai yana murmushi. "Wannan." Ta zira hannunta a gaban madubin, ta ɗauko turaren oud al'abyad. Feffesa masa ta yi sannan ta fesa ma kanta, ta miyar ta ajje tana fuskantarsa. "Mu kwanta ko?" "A ina?" Ya ce da ita a hankali yana kallon ta. "A can mana." Ta gwada masa gado, haɗe da yi masa hararar wasa. Isa ya yi bakin gadon, ya kwanta tare da takure kansa, sannan ita ma ta isa ta kwanta daga gefensa. Wani irin yanayi take ji sosai, mai cike da shauƙi da farin ciki. Sai a yanzu ne take daɗa tabbatarwa, cewa da gaske an ɗaura mata aure da Annur. Sakin murmushi ta yi a hankali ta zira hannunta bisa cikinsa, ta tallabo shi a jikinta. Wani irin yar! Ta ji a jikinta, hakan bai sa ta sake shi ba, sai ma ƙara rungume shi da ta yi tsam-tsam, tana jin yadda nutsuwa ke sauka a duniyarta. A haka barci yai awon gaba da su duka biyun, barci mai cike da mafarkai kala-kala, duka masu tsantsar daɗi da nishaɗi. Asubah da gari Marnoor. * Idanuwanshi tsaye suke ƙyam bisa ƴar madaidaiciyar wuƙar da ta yi aƙalla mintuna goma sha biyar a hannunsa. Hawaye yake saki, mai cike da ƙunar zuciya da tashin hankali. "Rayuwa ta juye min baki ɗaya. Na rasa duk wani farin ciki da jin daɗina. Walwala ta ƙaurace min. Mutuwa ce daidai ni a wannan lokacin, ita ya kamata a ce ta zo ta tafi da ni, sai dai kuma har yanzu ta ƙi zuwa, don haka dole ni na jawo ta da hanzari, ta zo inda nake." Ya saki kuka da ƙarfi, ba tare da ya ɗauke idanuwansa daga kan wuƙar ba. Kuka yake sosai har da shessheƙa, yana jin yadda zuciyarsa ke tafarfasa, take karanto masa cewa kashe kanshi ne kawai zai zame masa alkhairi, shi ne kawai zai saka ya samu sassauci. Duk wani ɓangare na zuciyarsa da zai ƙoƙarta kwaɓarsa tare da kawo masa haramcin mutum ya kashe kanshi, sai ya kwaɓe shi, inda ke ƙara tunzurasan kawai yake biye mawa. Da ƙarfi ya ɗaga wuƙar haɗe da caka ma cikinsa ita, ya saki wani irin razanannen ihu, tare da zubewa ƙasa. Sosai jini ke malala daga cikinsa, idanuwansa a rufe. Ihun Sans baki ɗaya sai da ya karwaɗe farfajiyar gidan, har ta ɓangaren da mai gadi yake. Sai dai kuma tazarar da ke akwai daga farfajiyar zuwa cikin gidan akwai ɗan tsayi, hakan ya sa mutanen cikin gidan ba za su ji ƙarar ba. Mallam Ya'ulle mai gadi ya ce da Habu mai wankin mota, "Kamar daga ɓangaren Annur fa wanann ihun ya fito." Habu cikin kiɗima ya ce, "Ko tantama babu daga can ne. Da alama ba lafiya." Suka miƙe su duka biyun, suka tinkari ɗakin Sans. A halin da suka gan shi ne suka daɗa gigita. Yadda jini yake kwance male-male a wurin, ga kuma Sans da ko alamar numfashi babu a tattare da shi. "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Habu maza-maza ka kira Yallaɓai da Hajiya, Allah dai ya sa yana raye." Cikin kuka sosai mallam Ya'ulle ke wannan maganar, yana kai kanshi saitin ƙirjin Sans, ko zai ji fitar numfashi. A guje Habu ya isa falon, ya samu Momy ce zaune, sai su Hanan da Janan da suka zo hutu yau. Dalilin ma da ya sa su Momy ɗin ba su koma gidan su Maryama wurin biki ba kenan a ranar. A yadda Momy ta ga Habu ne ya tabbatar mata da ba lafiya ba. Miƙewa ta yi cikin kiɗima, ta ce, "Habu me ya faru...?" Bai ko jira ta dire tambayar tata ba, ya ce, "Hajiya babu lafiya. Annur ga shi can kwance cikin jini, kamar ma ba ya numfashi ko kaɗan." Ido buɗe momy ta dafe kanta, da sauri da sauri ta ji gabanta na faɗuwa. Ta ce, "Habu me kake faɗa ne haka?" "Hajiya ba wannan ba ne ya kamata ki yi, sai an gaggauta kai shi asibiti, domin a ba shi taimakon gaggawa, idan ma yana raye kenan." Shi kanshi kuka yake sosai, su Hanan ma hankalinsu ya tashi, Janan ta nufi ɗakin Dady ta sanar masa. A kiɗime Dady ya fito shi ma, ko riga babu a jikinsa sai singlet, yana faɗin "Ku ba ni mukullin mota." A hakan ya fice zuwa ɗakin Sans, ya tarar mai gadi sai famar kuka yake, ya kasa zaune ya kasa tsaye. "Ya Salaam! Annur me ya faru haka? What's wrong with you? Cakar ka ta yi wuƙar? Sai dai haka kam. Mallam Ya'u ku taimaka ku kamo min shi a kai mota, insha Allahu Annur ba zai mutu ba, zai tashi da kafaɗunsa." Cicciɓarsa suka yi suka kai mota, a lokacin har su Momy da ke ta ruzgar kuka sun isa bakin Prado ɗin. Bayan an saka shi suka shisshiga ciki, kai tsaye suka nufi Nadda Hospital. * Sai shida da rabi ya samu damar tashi, kasantuwar hidimar biki akwai gajiya sosai. Da ƙyar ta iya buɗe idanuwanta, ta sauko daga bisa gadon a hankali, sannan ta nufi toilet. Alwalla ta ɗauro sannan ta fito tana tsane ruwan hannunta a jikin rigar barcinta ta silk. Hijabinta ta ɗauko ta saka sannan ta tada sallar, a lokacin har gari ya fara yin haske-haske. Bayan ta sallame ta yi addu'o'i sosai, sannan ta fara niyyar tashin Annur. Har ta ɗaga hannunta za ta ɗan bubbuga shi, sai kuma ta tuno cewa, psychologically ba a son tayar da mai mental illness daga barci. Sosai hakan ke ƙara rikita ƙwalwarsa, saboda an dakatar da wani jin daɗinsa. Fasawa ta yi, ta jawo blanket ta rufe shi, saboda sanyi-sanyin da ake yi, kasantuwar an kwana ana shara ruwan sama. Komawa ta yi ta kishingiɗa bisa tafkeken kafet ɗin da ke baje daga gefen gadon, sannan ta zaro wayarta da ke jikin caji. Text take son ta tura ma iyayenta na godiya, da kuma sauran mutanen arziƙi da ƙawayenta na ban-gajiya. Iyayen nata ta fara tsara ma text mai matuƙar ma'ana, ta musu godiya na hidima da ita da suka yi tun haihuwarta har izuwa girmanta. Sun ciyar da ita, shayar da ita, suturtar da ita, sannan kuma suka ilimantar da ita ba tare da gajiyawa ba. Sun ba ta duk wani farin ciki da ya kamata iyaye su ba ma yaransu, har ma sun zarce. Sun ba ta tarbiyya mai kyau, wacce ta zam abar alfahari ga kowa, ake son koyi da duk halayenta. Sannan a ƙarshe suka ba ta farin cikinta, ta hanyar aura mata mutumin da take da muradin taimaka masa, da kuma tsantsar ƙaunarsa. Tana gama rubuta text din ta sharr hawayen da suka sauko mata. Ta ɗan yi jim! Ba tare da ta sake kallon wayar ba, saboda jikinta da ya yi sanyi, iyayenta da kuma Hammad ƙaninta, kuma abokinta ta tuna, cewa ta rabu da su kenan fa sai dai idan ta je ganin gida. Ta daɗe a haka kafin ta wartsake, ta musu sending message ɗin a tare. Kawu Imrana ta fara rubuta ma nashi, na tsayuwar da ya yi ga rayuwarsu, tun ma kafin su zo duniya. Sannan a ƙarshe ya goyi bayanta ɗari bisa ɗari, ta hanyar tsayuwa tsayin-daka ganin an aura mata farin cikinta. Ba ta da hanyar biyansa, addua ce kawai za ta masa. Ta nemi gafararsa a kan butulce ma zaɓinsa da ta yi, ya yi haƙuri ya gafarta mata. Text guda ta rubuta na ban-gajiya, ta yi sharing ɗinsa ga duka contacts ɗinta. Datarta ta buɗe saboda ta jima ba ta hau charting ba. A hankali charts suka ringa shigo mata, wasu daga ciki na taya ta murna ne, mafi rinjaye dai groups ne da take, saƙuna da yawa saboda jimawar ta ba ta hau ba. Kamar wasa ta ga shigowar saƙon Dr. Hamdan, tamkar a mafarki haka ta shiga cikin saƙon nasa, ta hau karantawa. Ce mata ya yi ya ji ta shiru, kuma ya kira ta tun ranar da suka yi magana amma ba ta ɗauka ba. Tun bayan da suka yi maganar nan bai san dalili ba ya ji abun ya masa tsaye a rai, ya ji tausayin mara lafiyan sosai. Idan har za ta samu lokaci, to ta daure ta kawo shi Maidugurin, ya mata alƙawarin duba lafiyarsa sosai. Idan kuma tana ga kamar abun da sauƙi sosai, to ta jira shi, akwai Seminer da zai je Kano nan da sati uku, in ya samu yadda yake so zai zo Katsinar wurin wani abokinsa. Idan kuma bai samu zuwa ba, to sai su same shi a Kano ɗin. Sosai Maryama ta ji daɗin hakan, farin ciki ya kasa ɓoyuwa daga fuskarta, gani take kamar ma har Annur ɗinta ya warke ne. Saboda yadda Dr. Sandra ta rinƙa ƙawata Dr. Hamdan ta tabbatar cewa gwani ne. Miyar masa da saƙon ta yi, cewa za ta jira shi ɗin har ya zo, tunda dai ta bi shawarwarin Dr. Sandra sosai, ta kuma ga ci gaban hakan. Kashe datar ta yi bayan ta tabbatar saƙon ya je masa, sannan ta miƙe bisa ƙafafuwanta, tana jin yadda daɗi ke ziyartar zuciyarta. Kallon Annur ta yi a karo na biyu, ta saki murmushi, ganin yadda ya haƙiƙance barcinsa yake. Falo ta nufa kai tsaye, ta hau dudduba yadda komai na falon ya tsaru, sai ta ji ya ƙara birge ta sosai. Daga nan ta wuce ɗayan bed room ɗin, wanda ya kasance nata, shi ma ta sake duddubawa, komai ya yi tsaf gwanin ban shaawa. Ta fito kuma ta nufi kitchen. Haka ta zagaye gidan tsaf tana duba tsaruwarsa, kafin ta koma ɗakin Annur. Har a lokacin bai tashi ba, a bayyane ta furta, "Sai sharar barcinsa yake yana morewa. Kai ma kenan da babu gajiyar biki a tattare da kai." Ta cire hijabinta sannan ta shiga wanka. Bayan ta fito daga wankan ta wuce ɗakinta. Mai ta shafa sannan ta yi light make_up. Ta feshe jikinta da body spray lungu da saƙo, har a bayan kunnenta. Bayan ta gama ta ɗauki cotton bud ta goge bayan kunnen nata da shi. Bakin wardrobe ɗinta ta isa, ta fiddo wata atamfa kalar light blue, da aka ƙawata da manyan flowers kalar pink. Ɗinkin riga da skirt ne da suka bi jikinta, suka bayyana shape ɗinta sosai. Bayan ta saka ta ƙarisa gaban madubi, ta kalli kanta sosai sannan ta ɗaura ɗankwali. Turarukan oud kala kala ta feshe jikinta da su, ta saka takalma high heels ta bar ɗakin. Isar ta ɗakinsa ta same shi ya tashi, sai famar dube-dube yake, da alamu ita yake nema. Yana ganinta ya saki tattausan murmushi, yana motsa bakinsa. "Mi Amor ka tashi?" Bai san me take nufi da kalmar da ya ji ta kira san da shi ba, sai dai kai kawai da ya ɗaga mata, fuskarsa har yanzu ƙunshe da faraa. "Then, mu shiga toilet ka yi alwalla ko?" "Ban iya ba." Ya faɗa yana gyargyaɗi da kansa. "Mu je zan yi maka ne. Daga yanzu kullum zan rinƙa koya maka sallah. Insha Allahu sannu a hankali za ka iya. Mu je." Miƙewar kuwa ya yi, ya bi bayanta suka isa ban-ɗakin. Sai da ta matsa masa toothpaste a brush ta goge masa lungu da saƙo na bakinsa, sannan ta wanke mishi tas, ta masa alwallar. Tare suka fito, ta ce ya hau bisa kafet ɗin, duk abin da ya ga ta yi shi ma ya yi, ta saka hijabi. Raka'a biyu kuwa suka yi, sai famar waige-waige yake yi, sai ya saki murmushi, sai kuma ya ɗaure fuska, har suka ƙarisa sallar. Addua ta saka shi ya ma kanshi sosai, sannan ta ce, "Yanzu sai wanka ya rage ko?" Ya ɗaga mata kai. "To ina zuwa. Ban kunna heater ɗin ba ma." Ta shiga toilet ɗin. Knocking ta ji ana yi daga bakin ƙofa, ta gaggauta fitowa daga toilet ɗin ta isa ƙofar falo. Tana buɗewa ta ga Hammad ne da wata cousin ɗinta Aysha, hannuwansu riƙe da basket mai girma, sun kamo su biyun. Murmushi ta sakar musu, ta ce, "Sannun ku da zuwa ƙannena. Ku shigo." Ta yo gaba suka biyo bayanta. Zama suka yi bayan Aysha da Hammad sun azzo basket ɗin a bisa dinning table. "Ina kwana Yaya?" Suka faɗa a tare. "Lafiya ƙalau. Ya gida ya su Mama?" "Sun ce ma a gaishe ku." "Aikuwa muna amsawa." Ta isa gaban electronics, dama jiya su Jiddah sun haɗa mata komai, kunna musu kallo ta yi, African Magic Hausa ta kai musu, ana yin film ɗin Maula. "Ku yi kallo Sholie. Zan je in dawo. Idan ba ku karya ba ku ɗiba ku karya." Hammad ne ya ce, "Mun karya Yaya. Naku ne ku kaɗai ke da Yaya Noor." Dafa kansa ta yi sannan ta ce, "To shi kenan. Ku yi kallo kafin in dawo." Ta nufi ɗakin Annur ɗin. A yadda ta bar shi haka ta same shi, ya yi zaune a takure bakin gado, yana jiran ta. "Am sorry na bar ka Mi Amor. Su Hammad ne suka zo. Mu shiga ko?" Ta jawo light blue towel ɗinsa jikin ƙofa, ta riƙe a hannunta. Bayan sun shiga toilet ɗin ta rufe ƙofar, nan fa ake yin ta. Samun kanta ta yi da jin kunyar ganin tsiraicinsa, sosai ba kadan ba. Shi kam ko a jikinsa, ya hunce sannan ya tsuguna. Idonta ta rinƙa rurrufewa, sai idan za ta shafa sabulu take buɗe su, da haka dai aka yi wannan wanka, da ƙyar da jiɓin goshi. Idon a rufe ta ɗaura masa towel ɗin sannan suka fito. Ɗan ƙaramin towel ta ba shi cewa ya tsane ruwan jikinsa da shi, sannan ta ƙarisa gaban wardrobe ɗinsa ta fito masa da wani baƙin yadi mai matuƙar kyau. Feshe kayan da turare ta yi, har da boxer ɗinsa. Ta shafa masa mai, da mayukan turare a jikinsa, ta fara ƙoƙarin saka masa kayan. A nan ma an sha wata dagar, da ƙyar dai ta samu ta gama shirya shi, sai famar dariyar yaƙe yake yi, yana kallon kayan jikin nashi, yana tattaɓa su yana motsi da kai. "Kayanka ko? Suna da kyau sosai Mi Amor. Sun kuma karɓi jikinka. Amma ka san me? Ka fi kayan kyau. Sirrin kyawun kayan ma daga kai ne. Inda a ce wani namijin daban ne ya saka su to ba za su yi kyawun haka ba." Ta kama hannunsa suka ƙarisa falon, cike da ƙaunarsa, tana jin duniyarta na mata matuƙar daɗi. *** *My pipu ku yi maneji da wannan. Na san ya yi kaɗan, amma dai ku min uzuri. Kuma sai da na yi 1k words duka suka goge sai da na sako sabo.* *Ya kuka ji wannan shafin? Kun ga soyayyar Marnoor ta fara ƙarfafa sosai ko? Irin hakan shi ya fi komai daɗi.😍😘* *A wani ɓangaren kuma, mun ga yadda Sans ya luma ma cikinsa wuƙa, da nufin kashe kansa.* *Wanann wace irin damuwa ce mutum ke gare shi da har zai gwammaci ya rasa rayuwarsa? Duk wanda ya kashe kansa fa ya mutu kafiri, wutar Jahannama ita ce makomarsa.* *Ko Sans ɗin ya mutu? Alƙalamin Amrah kawai zai warware mana.😥😪* *My Sister na gode ƙwarai da haɗaɗɗiyar video da kika haɗa ma wannan littafin. Video fa ta yi kyau masha Allah! Kowa ya yaba. Allah ya saka miki da alkhairi ya bar zumunci.❤💃* *Kar a manta a rinƙa yi ana tunowa da danna ƴar tauraruwar nan mai kyau da daɗin taɓawa.😀* Thanks all. Pinky durling💞 RAZ 2 [9/21, 12:06 AM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taɓa zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 6⃣7⃣ Wattpad: PrincessAmrah *** Emergency aka karɓi Sans, aka shiga ciki da shi domin tabbatuwar yana raye ko ba ya raye? Idan yana raye to sai a ba shi taimakon gaggawa. Tun sadda aka shiga da shi hankalin su Dady bai kwanta ba. Momy sai zirga-zirga take, ba ta nan ba ta can, tana ta aikin zubar da ƙwalla. Sosai suke son sanin halin da Sans yake ciki. Hakan ya sa Dady ya kasa daurewa, bai jira an ba shi izini ba kawai ya afka cikin ɗakin. Ganin ya yi malaman asitin sun yi cincirindo a bakin wani gado, duk da bai ga wanda suka zagaye ɗin ba, amma ya tabbatar da cewa Annur ɗinsu ne. Hakan ya sa ya gaggauta isa inda suke, hankalinsa a tashe. Kallo ɗaya za ka ma Dady ka tabbatar cewa ba ya cikin nutsuwarsa. Saboda yadda duk ya bi ya koma tamkar zararre, rigar jikinsa ma a birkice ya saka ta, saboda har ma ya shiga mota daga shi sai singlet da gudu Janan ta koma ta ɗauko masa rigar ya saka. "Ya za ku bar ni a cikin duhu ku kasa fa min haƙiƙanin abin da yake damun yarona?" Ya faɗa a fusace, yana kallon yadda suke aiki bakin ƙoƙarinsu domin taro numfashinsa, kafin a fara yi masa ɗinki a cikin nasa. Babban likitan da ke wurin cikin tattausan lafazi ya dafa kafaɗar Dady, ya ce, "Ka kwantar da hankalinka Alhaji. Insha Allahu yaronka zai ci gaba da rayuwa kamar kowa, zai tashi da kafaɗunsa. Akwai bayanin da ya kamata na maka, amma ka yi haƙuri ka fita har mu shawo kan babban lamarin, sannan zan buƙaci ganawa da kai. Kar ka ji komai fa, da yardar Allah komai zai daidaita." Sai a sannan Dady ya ɗan samu nutsuwa. Ya sauke nannauyar ajiyar zuciya, ba tare da ya furta komai ba ya nufi barin ɗakin. Da sauri su Momy suka ƙarisa gabanshi, suna tambayarsa halin da Sans ɗin yake ciki. "Da ransa bai mutu ba. Suna can suna aiki a kansa sosai. Mu taru mu saka Annur ɗinmu a addua, ita ya fi buƙata daga gare mu a daidai wannan lokacin ba wai kuka ba." Yana gama faɗin haka ya koma bisa teburin da aka jera a reception ɗin ya zauna haɗe da rafka uban tagumi, yana ta famar ambaton sunan Allah daga bakinsa. Jin hakan ya sa su ɗin ma suka ɗan samu kwanciyar hankali. Amma duk da haka ba su daina yin kukan ba. Hanan da Janan suka zauna kusa da Dady, momy kam zaman ya gagare ta, zirga-zirga kawai take hannunta tallabe da bayanta tana hawaye tana addu'a a bakinta. * Kanta ta ɗora a saman cinyarsa. Fuskarta ƙunshe da fara'a, ta jawo hannunsa saitin kanta tana faɗin, "Mi Amor kai fa nake jira don Allah. Ka ringa bubbuɗa tsakiyar gashin kana duba inda ke da dandruff sai ka kankare min." Saurarenta kawai yake, amma fa ba ya fahimtar komai, sai murmushin da yake saki shi ma ɗin. Ta san da hakan sarai, ta san cewa ba ya gane abin da take nufi, amma da gan-gan take komai, tana son ƙara kusancin zukatansu ne. Tashi ta yi zaune haɗe da girgiza kanta, gashinta da ya barbazu bisa fuskarta ya koma ya kwanta har bisa gadon bayanta. Ribbon ɗinta ta sa ta ƙulle gashin, sannan ta shafa mai a gaba-gaban ya ƙara kwanciya, kwantaccen gashin goshinta ya kwanta luf. "Yah Noor ka san me?" Ya girgiza mata kai. "Ina ƙaunarka sosai." Ta saki sassanyan murmushi. "Kai ma ba za ka ce kana ƙaunata ba?" Ta ɗan turo baki alamun shagwaɓa. Kallon ta kawai yake tana daɗa birge shi. Sai dai kuma bakinsa ba zai taɓa iya furta yana son kowa ba face Amrah. Duk yadda ya buɗe baki da nufin faɗa wa Maryama cewa yana son ta, sai bakin ya gagara faɗi, ya ambaci sunanta da Amrah. "Kana jin kunya ta ne? Well. Zo ga kunnena ka raɗa min a ciki. Don Allah for once dai ka furta min cewa kana so na. Zan ji daɗi sosai Mi amor" Ta kanga masa kunnen nata, tana sauraren abin da zai faɗa mata. Ji ta yi ya yi murmushi a kunnen nata, ya ce, "Amrah nake so!" Janye kunnenta ta yi a fusace, ranta in ya yi dubu ya ɓaci. Ta fara jin haushi sosai, da kuma kishi da ke nuƙurƙusar zuciyarta. Ita kanta ba ta san yadda akai ta kamu da kishin matacciyar da ba ta duniyar ba ma. "Yah Noor ba zan ƙara cewa ina son ka ba tunda har yau na gagara ka ambata kana so na. Haba don Allah! Kullum dai Amrah! Amrah! Amrah!? Ya kamata by now a ce ta fita daga ranka. Matar da ba ta duniyar baki ɗaya, amma ta gagara fita daga bakinka. Haba mana ka samu ka fitar da ita daga ranka ko za ka samu dawowa a cikin hankalinka..." Ta kwantar da muryarta a daidai sadda hawaye ke fita daga idanuwanta, ta ce, "Don girman Allah Yah Noor ka so ni koda rabi-rabin ƙaunar da nake maka ne. Ya kamata a ce ka farga, ka fitar da Amrah daga zuciyarka. No more Amrah in your life yah Noor. No more Amrah in this world. Amrah ta tafi inda ba a dawowa. Ta tafi inda mu ɗin ma za mu je mu same ta, amma ba dai ita ta dawo ta same mu ba. Na sani, cewa Amrah masoyiyarka ce ta gaske. Ka ƙaunace ta, kamar yadda ita ma ɗin ta ƙaunace ka. Kun yi soyayya ta tsakani da Allah, mai cike da tsafta da yarda da juna. Amrah was your first love, amma kar ka ɗauka cewa ita ce last love ɗinka. Saboda har yanzu kana da masu yi maka irin ƙaunar da Amrah ke maka." Ta dakata daga nan, tana kuka sosai mai cike da tashin hankali, duniyarta na mata juyin waina, kamar yadda zuciyarta ke juyewa daga farin-ciki zuwa baƙin-ciki. Kanta a duƙe yake ƙasa, tana sakin kuka mai cike da tashin hankali, kamar wasa ta ringa jiyo shessheƙar kukansa, ta gaggauta ɗago da kanta, ta ɗora idanuwanta a bisa kyakkyawar fuskarsa da ruwan hawaye ya gama wankewa. Kallon sa take cike da mamaki. Me ya sa shi kuka? Ta tambayi kanta. Ganin yadda bil-haƙƙi yake kuka ne ya daɗa tayar mata da hankali. Kuka yake mai cike da tashin hankali, jikinsa na karkarwa, idanuwansa sun kaɗa sun yi jajur a cikin ɗan taƙi kaɗan. Ƙasa ya ƙura ma ido yana kallon wuri guda, hannunsa ɗaya dafe da kansa, ɗayan kuma ya ɗora a bisa cinyarsa, ya dunƙule shi. Gyaɗa kanta ta hau yi, tare da ƙarfafa kukanta, tana faɗin, "Ni ce? Don Allah ka yi haƙuri ka yafe min. Ban san cewa abun zai maka zafi har haka ba. Ba zan so Allah ya rubuta min zunubi ta dalilin saɓa maka ba. Wajibi ne a gare ni na faranta maka, na ba ka duk wani farin-ciki kamar yadda na yi alƙawari." Ta dakata daga nan, ta ci gaba da binsa da kallo. Ji ta yi cikin sanyin murya ya fara magana, "Amrah nake so! Amrah ce kaɗai a cikin zuciyata. Amrah me ya sa za ki min haka? Me ya sa za ki tafi ki bar ni? Ina ƙaunarki Amrah. Ke ce rayuwata. A kullum da ƙaunarki nake kwana nake tashi. Soyayyarki ke ɗawainiya da duk wata gaɓa da ke cikin gangar jikina. Ki dawo gare ni Amrah. Ki zo ki tallafi rayuwata Amrah. Ki zo ki bayyanawa duniya cewa ke kaɗai nake so, kamar yadda ke ma ni kaɗai kike so..." Kuka sosai yake yi, a hankali yana tuno wasu abubuwan, wanda dama yakan tuno su, sai dai wasu lokutan da zarar ya tuno su, sai kanshi ya hau sarawa, tare da manta komai da ya fara tunowar. Sosai take mamakin Annur. Sau da dama yakan yi abubuwa irin na masu hankali. Yakan yi kalamai masu sanyaya zukatan ma'abota soyayya. Duk yadda yake gwada yana son ta, lokaci kaɗan zai birkice mata, tamkar ma bai taɓa ganin ta ba. Abun nan yana ci mata tuwo a akushi. Tana shiga tsantsar damuwa a duk sadda irin hakan ta faru. Sai dai kuma tun da ta san shi, daga lokacin da ta ɗauko shi daga Maraɗi ta dawo da shi gidansu, ba ta taɓa ganin shi ya yi irin wannan kukan ba. Tabbas kalaman ba baƙi ba ne a gare ta, to sai dai abin da ya tayar mata da hankali yadda yake kuka riris, jikinsa na ta famar karkarwa. Hannunsa ta kama duka biyun, ta damƙe su a cikin nata. Sosai take jin nutsuwa na saukar mata. A duk sadda za ta taɓa shi, sai ta samun sauyin yanayi irin haka. Sai ta ji yadda ƙaunarsa ke ɗaukar ta tana kai ta can wata duniyar ta daban, duniyar da masoya ne zallah a cikin ta. Ji ta yi hannunsa zafi rau, saɓanin yadda ta taɓa su ɗazu sadda tana kwance a cinyarsa. Cikin damuwa ta ce, "Ka gani ko? Ga shi nan wannan kukan da kake ya sakar maka zazzaɓi. Ka ji yadda jikinka ya yi zafi sosai Yah Noor. Don Allah ka daina kukan nan. Wallahi ba zan sake tayar maka da irin wannan maganar ba. Na maka alƙawari." Bai daina kukan ba, sai dai ya rage ƴarfinsa. A hankali ta isar da gangar jikinta gare shi, ta haɗa jikinsu, tana jin yadda bugun zuciyarsa ke tafiya. Hannuwanta ta zira ta rungumi bayanshi, ta ɗora fuskarta a bisa kafaɗarsa. Ji ta yi nutsuwa na saukar mata, kamar yadda shi ɗin ma a nashi ɓangaren hakan ne. Shiru ya yi da kukan da yake yi, bugun zuciyarsa na daidaita, yayin da yake jin duniyarsa ta damuwa na rikiɗewa izuwa ta farin-ciki. Jin ya dakata da kukan ya sa cikin saukar da murya ta ce, "Ka san yadda zuciyata take ƙuntata a duk lokacin da zan ga ɗigar hawayenka ɗaya a bisa kumatunka? Ka san irin halin da nake shiga a duk sadda kake cikin halin ƙunci? Sosai nake shiga tararrabi a duk sadda zan gan ka takure alamun rashin walwala. Ka taimaka ka daina, matuƙar ba so kake a zo a kwashi gawata daga gidan nan ba." Saukar ajiyar zuciyarsa kawai take ji. Tana jin yadda ya langaɓar da kansa a tata kafaɗar, ya sadaukar da kaf gangar jikinsa gare ta. Sun jima a haka, har sai da dukkaninsu suka samu wadatacciyar nutsuwa, kafin ta raba jikinsu da juna, ta ɗora idanuwanta a kan rinannun nashi idanuwan, tana bin sa da kallo. Murmushi ta ƙirƙiro kafin a hankali ta ce, "Ya isa to ai, komai ya wuce. Bari in tashi in kawo maka abinci." Kanshi ya ɗaga mata. "To ai ban ga ka yi murnushi ba." Muenushin ya saki wanda har sai da hakoransa suka bayyana. Sosai ta ji dadi, wani sanyi ta ji ya dira a cikin zuciyarta. Kai tsaye ta nufin kitchen domin ta kawo masa abincin. Vegetable noodle ce ta dafa, kasantuwar ta dawo exam ne a ƙurarren lokaci, saboda yau suka fara kuma da guda biyu suka fara. A plate ɗaya ta zubo musu, ta duba pepper soup ɗin da ta ɗora a wuta saura ƙiris ruwan ciki ya ƙare. Da sauri ta gaggauta kashe gas ɗin, sannan ta zuba ruwa madaidaici ta motsa, ta kuma kunna gas ɗin amma ta rage ƙarfin wutar. Fork guda ɗaya ta saka a plate ɗin, sai kuma ta ɗora spoon ɗaya, ta nufi fitowa. A gabanshi ta ajje, sannan ta ce, "Bari in kawo mana drink." Ta koma ta ɗauko kwalbar blue cocktail guda da cups guda biyu, ta fito. A baki ta ringa ba shi abinci a hankali yana ci. Sai ya ringa kallon ta yana murmushi, tamkar ba shi ne ya gama rusar kuka yanzu ba. Da haka har suka ƙoshi, ta zuzzuba drink ɗin a cup, da kanshi ya kai baki ya sha nashi, sai da ya shanye duka sannan ya ajje cup ɗin. Ita ma ta sha. Kwashe kayan ta yi duka, kafin ta dawo kusa da shi, ta gyaggyara wurin ta feshe da tangerine freshner. Bayan ta gama duka ta jawo handout ɗinta da take dubawa tun sadda take kwance a cinyarsa, ta hau dudduba kaɗan-kaɗan, shi kuma ta kunna masa kallo, tashar Zee World. *** Kakkausan murmushi ta sakar masa a lokacin da ta same shi a ɗakin. Da nashi murmushin ya tarbe ta, cikin idanuwansa nata idon suke, har sadda ta iso gare shi. "Har bakin sun tahi?" Ya tambaye ta, bayan ya haɗa jikinsa da nata. "Uhm sun tahi. Sun ce ma in gaishe ka." Ta ƙoƙarta ɓamɓare jikinta da nashi. "Mi halan rowa za ki yi mini?" Gyaɗa kanta ta yi ta murmusa. "Lokacin sallah dai yak kusan yi." Ɗan taɓe bakinsa ya yi, ya ce, "Hakanan hwa. Bari in nuhi masallaci to." Ya miƙe haɗe da ɗaukar hularsa daga bakin gado ya saka. "A yi min addu'a." Hannunsa na dama ta kama ta saka a cikin nashi, ta ce, "Allah ya sa a dawo lahiya. A yi mana addua." "Insha Allahu. Amma wace iri kika son na yi miki?" Sai da ta ɗan yi shiru alamar tunani, kafin ta ce, "Zaman lahiya da zuri'a mai albarka." "To na yi alƙawarin zan yi. Amma hwa ni ma ina da buƙatar wani abu." "Mi halan?" Ta tambaye shi cikin yatsinar fuska. "Kawo kunnenki ki jiya." Ta kanga masa kunnen nata. Magana ya mata ƙasa-ƙasa, wadda duk iya ƙwa-ƙwar mutum ba zai taɓa jin abin da ya faɗa mata ba. Da alama dai zance ne na ma'aurata. Murmushi kawai ta saki haɗe da gyaɗa masa kanta, ta ce, "To na jiya. A dawo lahiya." Ya fice daga ɗakin yana dariya, haka ita ɗin ma dariyar take. Kitchen ta nufa, farar shinkafa ce take dafawa, koda ta duba har ta dahu, ruwa kaɗan ne kawai bai tsane ba. Ta duba miyar ita ma ta dahu. Ta sauke sannan ta kashe reshore ɗin. A flask ta juye miyar sanann ta bar ta buɗe don ta ɗan sha iska. Kafin nan har ruwan shinkafar ya tsane, ta sauke shi ma ta kashe ƴar bouncing burner ɗin, ta kwashe shinkafar a food flask babbar ta miyar. Kafin Mahmouda ya dawo daga masallaci Fiddou ta gama shirya komai ta kai falo bisa kafet ta ajje. Dama ta yi wankanta, kaya kawai ta sauya, daga atamfa zuwa wata doguwar rigat roba, wadda ta kame jikinta. Kanta babu ɗankwali, sai yalwataccen gashinta da ta faka ya zuba har bisa gadon bayanta. Tana fitowa ta same shi ya dawo yana jiran ta. Da sauri ta ƙarisa gabansa tana masa sannu da zuwa. "Madem ke yi kyau sosai hwa. Irin wanann kwalliya ai sai ki saka na kasa cin abinci." Harararsa a wasa ta yi, ta ce, "Aikam ba zan so mijina ya zauna da yunwa ba. Saboda haka bari in hanzarta zuwa in cire kayan in sako wanda ba za su hana maka cin abinci ba." Ta nufi barin jikinsa. Jawo ta ya yi da hanzari, ta faɗo bisa jikinsa. "Wa ya hwaɗi miki irin haka nake nuhi? Ai wannan kaya irinsu ne nake so ki rinƙa saka min duk sadda nake gida." "To na ji. Ga abinci nan." Ta ƙarisa bisa kafet ɗin, shi ma ya iso kusa da ita ya zauna. Serving ɗinsu ta yi. Ciyar da junansu suka hau yi cike da soyayya da ƙaunar juna, sai da suka ji su sun yi jim sannan ta kwashe kayan haɗe da dawowa. "To kyan alƙawari cikawa. Na yi miki addua don haka ke ma sai ki cika naki alƙawarin." Maficin hannunta ta duke sa da shi, ta ce, "Halan dai ba ka gajiya?" "Har abada! In dai da ke ne." Miƙewa suka yi suka nufi bedroom maƙale da junansu. *** Cike da shauƙin ƙauna take waya, tana yi tana ɗan lumshe idanuwanta, tana sakin wani tausassan murmushi. Tsabar jin daɗin wayar da take ya sa ta ringa tsigar stones ɗin lace ɗinta da aka ƙawata shi da su. Ita kanta ba ta san tana yi ba, har sai daga baya ta ankare. Cikin mamaki ta ce, "D me ka san me ka ja min kuwa?" "A'a J me sai kin faɗa." "Uhm. In faɗa maka kaf stones ɗin da aka ma kayan jikina ado da su na bi na cire du, duk ban san na yi ba sai yanzu na ankare." Dariya sosai ya yi mai sauti. Ya ce, "Ah to komai ya yi daidai. Hakan ya tabbatar min da cewa kina jin daɗin wayar da muke yi ɗin." "Uhm, to ni dai sai ka biya ni, tunda dai kai ne silah." Cikin shagwaɓa ta yi maganar, har can cikin kunnuwansa ya ji dirar sautin nata. Ya ɗan lumshe idanuwansa, cike da bege ya ce, "J me kin cika rigima. Na ji to zan biya ki. Just count, in the next 2 or 3 months zan ninka miki wannan ɗin ma." Tamkar tana a gabanshi haka ta harare shi, ta ɗora hannuwanta a daidai saitin zuciyarta, ji take yadda rijiyar ƙauna ke gudanya a cikin zuciyar tata, tamkar ta sa hannu ta yakito ta, ta gan ta da ido, ta yadda za ta ƙara azama wurin ƙaunarsa. "D me ka san me?" "Sai kin faɗa dai tukuna zan sani." "Jiya bayan ka tafi Abbana ya kira ni. A gaban Mami ya ce wai ya ji daɗi sosai ta yadda ya gan ka mai ladabi da girmama na gaba da kai. Ya ce wai ya tabbatar ba zai yi asarar aura maka ni ba." "J me am so much happy. Ashe har haka nake da daraja a wurin Abbah?" "Ehh mana. Amma don Allah D me kar ka watsan ƙasa a ido. Kamar yadda kaken nan a yanzu, ina so ka ƙara azama wurin darajta iyayena. Sosai za ka ƙara siye zuciyar Jiddah..." Bai bari ta ƙarisa ba da murmushi ya ce, "Na riga da na gama saye zuciyar Jiddah. Kina nufin akwai sauran wata tsoka a cikin zuciyarki wacce ƙauna ta ba ta gama mamaye ta ba?" "Babu." Ta faɗa a hankali. "I know, Jiddah. I've trust on you. Sosai na yarda da ƙaunar da kike min. Haƙiƙa ni ɗin na zama mai sa'ar rayuwa, da ya kasance cikin kwanaki ƙalilan na gama siye zuciyar matata Jiddah. Ina fatar ɗorewar wannan soyayya tamu, har jikokinmu." "Ni ma ina fatar hakan Yayana. Abu ɗaya ne kacal ya rage mana a yanzu kam." "Mene shi?" Ya gaggauta tambayarta. "Wannan zazzafin kishin naka nake so ka rage shi D me. Na sani cewa ba abu ba ne mai sauƙi, domin kuwa shi kishi halitta ne daga Allah. Sannan kuma sai kana son abu ne har kake yin kishinsa. Amma a hakan nake so ka daure, ka rinƙa yaƙar zuciyarka, ka tausashe ta a duk sadda ta ƙoƙarta riya maka wani abu. Wani abun har da shaiɗan, zai yi yunƙurin ganin ya yaƙi zuciyarka, har ya haddasa fitina a tsakanin masoya. Don haka sai ka ba shi kunya. Duk lokacin da ya so riya maka wani abu, ka gaggauta korarsa, insha Allahu komai zai daidaita." Ajiyar zuciya ya sauke Deedah, ya ce, "Maganarki gaskiya ce Jiddah. Insha Allahu zan yi ƙoƙarin ganin komai ya tafi yadda ya kamata. Duk da cewa a yanzun ma na rage, kuma ina ma kan ragewa. Da yardar Allah komai zai zamto kamar ba a yi ba. Za ki same ni mutum mai kishi amma saisa-saisa." "Yauwa sweetheart. Am so glad hearing that. I really really love you my angel." "I love you too habibty. Ki samu ki kwanta ko?" "Yanzu kuwa D me." "Oya tell me something nice." "You are my husband, by Allah's grace." "Thanks and stay cool dear." Ya kashe wayar. Bayan ta janye wayar daga kunnenta ta manna mata kiss. A ranta tana jinjina yadda Deedah ya iya saye zuciyar mace. Sosai ya san hanyoyi da salo-salo na soyayya. Tana ji a ranta yanzu ta fara soyayya. Domin kuwa tarayyarta da Tahir ba wani abun arziƙi ne ta tsinta a ciki ba. Duk da cewa tana son Tahir sosai, amma ita kanta ta san akwai matsala tsakaninta da shi. Saboda sam Tahir bai da caring, bai damu da ya kula da ita ba. A rana so ɗaya tal suke waya, shi ma kuma sai idan zai kwanta ne zai kira ta, cewa zai kwanta gobe akwai aiki. Idan kuwa cikin weekend ne, tana samu har da rana su yi waya, amma da zarar sun fara za ta ji muryar ƙannenshi cewa ya zo ana kiranshi. Shi ne babba a gidansu hakan ya sa duk wasu responsibilies suka haye masa, tunda mahaifinsa ba wani mazauni ba ne. Dafe zuciyarta ta yi tunowar da ta yi da Tahir. Sai kuma ta ji tamkar ta famo tabon raunin da ya mata na ƙaunarsa ne a cikin zuciyarta. Tana cikin haka ta ji ƙarar shigowar text message. Ta ɗauka ta duba. Deedah ne ya turo mata text mai matuƙar daɗi da sanyaya zukatan ma'abota soyayya. Murmushi ta saki a sadda take karantawar, take ta manta da wani tunanin Tahir da take yi. * Idanuwansa na bisa fuskar likitan, tun daga sadda ya dawo Office ɗinsa ya nemi ganawa da shi. Ɗago kansa ya yi likitan, cikin sanyin murya haɗe da girmamawa, ya fara yi wa Dady bayani. "Akwai matsalar da yaron yake a cikin ta ne?" Shiru Dady ya yi yana nazari, kafin ya ce, "A iya sani na dai babu." "Ɗan ƙara tunawa dai." Shiru ya yi na tsayin lokaci, kusan minti biyar da ɗoriyar seconds, sannan ya ce, "To. Ya dai yi rashin babban abokinsa, ko in ce amininsa a kwanaki kaɗan da suka gabata. To wannan mutuwar sosai ta firgiza shi, ya kuma rasa sukuninsa. Tabbas, sai ma yanzu na tuna." Ɗan taunar leɓonsa ya yi likitan. Ya ce, "Kuma kana ganin wannan dalilin har zai iya zama silar da zai yi yunƙurin kashe kanshi?" Cikin kiɗima Dady ya miƙe tsaye. Idanuwansa a buɗe yake faɗin, "Dr. What are you saying? Kana nufin Annur ya yi attempting kashe kansa ne?" Kai kawai likitan ya ɗaga masa. "Calm down Alhaji. Koma ka zauna please." Komawar kuwa ya yi ya zauna, har yanzu bai daina mamaki ba. Bai ga dalilin da zai sa Annur ɗinsa ya yi yunƙurin kashe kansa ba. Bai rasa gata ba, haka kuma ba iyayensa ba ne suka mutu. Shin mutuwar Farouk Sardauna kawai za ta iya saka Annur yunƙurin barin duniyarsa? "A yadda result na hoton cikinsa ya nunar, wani abu mai kaifi ko kuma tsini ya shiga a cikin ne, wanda har ya tsinka wasu daga cikin kayan cikinsa. Tunda nake a rayuurata ban taɓa ganin wanda hakan ta faru da shi kuma ya ci gaba da rayuwarsa ba. Da zarar wasu daga cikin kayan ciki an ƙilla su, to a take mutum zai bar duniyarsa. Amma sai ga shi shi Allah ya iyakantar da abun, ba tare da ya mutu ba. A gaskiya ba zan ɓoye maka komai ba, duk wani taimako da zan iya yi na yi shi, na ba shi taimakon gaggawa. Abin da ya dace in dai kuna da hali, to kawai ku fitar da shi ƙasar waje, hakan zai fiye muku sauƙi. Sannan kuma, a duk sadda yaron ya farfaɗo, don Allah ku lallaɓa shi, ku binciki damuwar da yake a cikinta, cikin ruwan sanyi. Kar ku masa da zafi, a halin da yake ciki na tabbata zai buƙaci a taushi zuciyarsa. Saboda duk wanda za ku ga ya yi attempting kisan kansa, lallai ba ƙaramar damuwa ba ce yake a cikinta." Ya dakata daga nan yana kallon Dady. Ƙwalla ya ga Dadyn na matsowa daga idanuwansa. Cikin murya mai nuna damuwa ya ce, "Annur why? Why did you choose to kill yourself? Me ya yi zafi haka? Wannan wace irin damuwa ce kake cikinta, wacce ta gagara ka fito fili ka faɗa ma iyayenka ita?" Ya sake share guntuwar ƙwallarsa. "Ka kwantar da hankalinka Alhaji. Ai komai ma ya zo da sauƙi, tunda dai an samu ya farfaɗo. Abin da ya sa na faɗa maka ya kamata a fitar da shi waje, saboda su ɗin akwai na'urorin da suke amfani da su ga irin wannan matsalolin da mu ba mu da su gaskiya. Idan ma kuma akwai, to za a ɓata lokaci ne sosai, har ciwon nashi ya tsananta." "Babu komai Dr. Thank you very much. Insha Allahu za a fitar da shi, gobe idan Allah ya kai mu." "To Alhaji. Zan ba ka wani kati, in da hali ku kai shi India, ina da wani aboki a can, ya san aikin sosai, tunda ɓangaren neurology ya yi karatunsa. Insha Allahu zai ba ku duk wani taimako da ya kamata." Dady ya miƙa ma Dr. Hannu, ya ce, "Thank you once again Dr. I really appreciated. Gobe idan na kammala komai na tafiyar insha Allahu sai mu dawo mu tafi da shi." Ya miƙe. Addua da fatar alkhairi likitan ya masa, kafin Dady ya fice daga office ɗin. Ya samu su Momy a inda ya bar su. Da sauri Momy ta tare shi cikin kuka ta ce, "Alhaji ya kuka yi da shi?" Bayan ya kama hannunta sun zauna ne, ya fara ƙoƙarin fahimtar da ita cewa, "Annur ya ji sauƙi sosai, kuma da izinin Allah zai tashi da kafaɗunsa. Likitan ya ba ni shawara cewa mu fitar da shi ƙasar waje, ta yadda komai nashi zai samu daidatuwa." "Alhaji har yanzu ban ji haƙiƙanin abin da yake damun yarona ba. Don Allah ka sanar da ni." Gyaɗa kansa ya yi cike da tausayinta. Ya ce, "Annur wuƙa ya luma wa cikinsa da nufin kashe kansa har lahira. Shi ne abun ya tsaya a haka, bai ƙarisa mutuwa ba..." Bai rufe ba ki ba Momy ta zube ƙasa da ƙarfi tim! Kake ji. Da sauri Hanan da Janan suka yo kanta. Dady kuma ya hau kiran sunanta yana fifita ta da haɓar rigarsa, amma ko motsi bai ga ta yi ba. Hakan ya sa ya gwada ma Hanan nurses station cewa ta hanzarta kiran malaman jinya domin su ba ta taimakon gaggawa. Abin da ya faru ɗin kuwa kenan. Ta faɗa musu suka zo da gado aka ɗora Momy a kai, suka nufi Emergency da ita. Abun mamaki, ga gadonta ga kuma gadon Sans, haka suka jera. Shi an maƙala masa oxygen domin taimaka masa wurin numfashi. Ita kuma nurses sun hau kanta, suna ba ta agaji. Kusan minti talatin ta ɗauka sannan ta saki nannauyar ajiyar zuciya, kafin ta buɗe idonta da hawaye ya gama cika su, bayan kuma wanda ya bushe. "Me ya sa Annur ɗina zai yi yunƙurin kashe kansa? Ina tsananin ƙaunarka, da dukkanin zuciyata. Don Allah kar ka tafi ka bar ni..." Karaf ta ɗora idanuwanta ga Annur da ke kwance a gado. Yunƙurin tashi ta yi amma ta kasa. Wata nurse ta ce mata, "Sister ki yi haƙuri ki kwanta. Ki kuma cire wa kanki damuwar nan. BP ɗin ki ya hau sosai, yanzu haka yana 170 ne. Don haka sai kin sauƙaƙa wa zuciyarki." Gyaɗa kanta ta yi cikin kuka ta ce, "Ku kira min Alhaji." Ɗaya daga cikinsu ce ta garzaya waje ta sanar da Dady cewa patient ɗin tana son ganin shi. Da hanzari ya bi bayanta, suka shiga ɗakin tare. Ga Annur idonshi ya fara sauka, ya tausaya masa matuƙa, sannan ya juya ga Momy bayan ya isa gabanta. "Alhaji..." Ta faɗa cikin muryar kuka. "Ka taimake ni ka ceto min rayuwar ɗana." "Ba ni da ikon cetowa Suhaila. Allah ne kaɗai mai ceto. Mu namu sai dai addua kawai." "Na san da hakan Alhaji. Amma kana da kuɗin da za ka iya kai Annur ɗina koma wacce ƙasa ce. Ba na so na rasa shi, shi kaɗai ne ɗana namiji, ina son ganin ya ajje tashi zuri'ar..." Ta ƙarisa zancen da kuka sosai. "Kar ki damu Suhaila. Insha Allahu in dai kuɗi na aiki, to daga kwanan yau Annur ba zai kuma yin wani a ƙasar nan ba. Da izinin Allah za a kai shi India, zai samu lafiya. Amma fa sai kin tsaida addua, kin riƙe ta tam! Saboda babu mai warkarwa face Allah maɗaukakin sarki." Kanta ta ɗaga masa tana jin daɗi sosai. Ya ce, "Dare ya riga da ya yi, bari in kira Islam in sanar da ita, saboda Hanan da Janan nan ya kamata su kwana, ni ɗin ma haka, saboda Annur." Kanta ta gyaɗa masa, ta ce, "Za ka tayar mata da hankali ne a cikin daren nan. A bari har safe, sannan sai ka kira ta." Kai ya ɗaga mata, sannan ya mata fatar samun sauƙi, ya koma waje domin gabatar da sallolin da ke bisa kanshi. Babu magrib, ga shi har an kira isha. * Washe gari da safe ta kama talata. Tun da sassafe Dady ya kira Dr. Islam ya sanar da ita. Sosai ta tashi hankalinta, ta shirya Abdul, tunda hutun makaranta suke dama. Ta sanar ma mijinta sannan suka wuce Nadda Specialist Hospital. Sai bayan ta je ne Dady ya musu sallama cewa zai tafi ya fara shirye shiryen tafiya. Gida ya fara nufa, ya yi wanka sannan ya wuce ɗakin Annur, cikin kayansa yake laluben inda zai ga epassport ɗinsa. Bai gan shi ba. Hakan ya ba shi damar sake bincikar lakokinsa baki ɗaya. A nan ya ci karo da wani diary, kalar light blue, girmansa madaidaici ne. Wata zuciyarsa ce ta kitsa masa cewa ya buɗe, wata kuwa na ce mishi kar ya buɗe, sirrin yaro ne a ciki, sannan kuma ba abin da ya kawo shi ba kenan. Har ya miyar ya ajje, kuma dai ya sake ɗaukowa, ya buɗe shafin farko. Bama Local Government, Borno State. Abin da ya gani kenan a head line ɗin. Bai tsaya sake karanta komai ba, kawai ya rufe sannan ya miyar. Bincika ya ci gaba da yi, a lakar ƙasa ya ci karo da epassport ɗin, ya saki ajiyar zuciya haɗe da yin hamdala. Barin ɗakin ya yi ya koma mota, already ya ɗauko nashi epassport ɗin dama. A cikin wannan yinin ya kammala komai. Ya so a ce a ranar za su tafi, saboda ko kaɗan bai so su ƙara kwana a Nigeria ba. Amma sai Allah bai nufa ba. Aka ce sai gobe da misalin biyar na yamma sannan jirgin nasu zai tashi. Sai da ya musu siyayya sosai sannan ya koma asibitin. Har komawarsa yadda ya bar Sans haka yake. Ya dai samu tabbaci cewa sauƙi ne. Sai dai zuciyarsa ta kasa aminta. Saboda yadda yake ɗin, tamkar wanda ke cikin Coma. Bayan ya duba shi ne ya masa addua sosai, sannan ya wuce Amenity, saboda can aka miyar da Momy, tunda dai ta samu sauƙi sosai. * Washe gari da sassafe Dady ya gama da Dr. Safwan. Ya bashi katin da ya ce, sannan aka ba su sallama duka suka rankaya zuwa gida. Kayanshi Annur su Hanan suka haɗa masa a wata ƴar travelling bag. Sannan suka rufo masa ɗakin nasa, suka nufo falo. A lokacin Momy ma ta gama haɗa na Dady. Daga nan suka rankaya mota, suka nufi Kano, saboda daga can ne jirgin zai tashi. Uku da rabi na yamma ta musu a Airport ɗin Aminu Kano. Sans na a bayan motar Prado da aka kwantar da shi, mai gadinsu ya tuƙo motar sai Abba a kujerar zaman banza. A nan suka jira har lokacin tashin jirgin yayi, can Dady ya isa ya sanar da su halin da Sans yake ciki, sai ga su da gado aka zo aka ɗora shi a kai, sannan aka kai shi cikin jirgin. Biyar da minti goma jirgin nasu ya lula sai babban birnin Mumbai, ƙasar India. Momy ta sha kuka, su Janan na taya ta. Hotel suka nema suka kwana, sannnan washe gari suka nufi komawa Katsina. * Dressing ta yi, ta saka riga da skirt na atamfa, da zira hijabinta har ƙasa. Kusa da shi ta ƙarisa, ta riƙe masa hannu cikin murmushi ta ce, "Yah Noor ni zan tafi. Ga kalacinka nan duka na jera maka. Na zuba maka tea kar ya huce ga shi nan. Komai na zuba ka sauko ka ci. Lokaci ya ƙure min ne ba zan samu zama in karya ba. Exam ɗin ta ƙarfe takwas ce." Bai ce komai ba face murmushin nan nasa da yake saki a kodayaushe. Ya ziro ƙafafuwansa daga bisa gadon zuwa ƙasa, sannan ya miƙe tsaye a bisa ƙafafuwansa. "Ai dai za ka iya goge ma kanka baki ko?" Ya ɗaga mata kai. "To ka goge sannan ka yi alwallar da na koya maka. Idan ka fito sai ka yi sallah ka karya. Insha Allahu zuwa azahar zan dawo, sai na maka wanka." Ya sake ɗaga mata kai. Ta sakar mishi murmushi, sannan ta ɗauki jakarta da ATM card, saboda Abbah ya turo mata kuɗin zuwa makaranta, da kuma na cefane. Ɗaga masa hannu ta yi sannan ta fice, shi kuma ya nufi ban-ɗakin don ya gabatar da brush da kuma alwalla. Ya dawo bayan ya tabbatar da ta fita, sannan a hankali ya jawo wata ƴar drowa da ke jikin gado, inda ya ga Maryamar ta jefa karikitan da aka kawo mata daga gida, na Annur ɗin. Wannan zoben ya gani a naɗe kamar yadda ta mishi tun waccan ranar, a hankali ya buɗe shi, ya ƙura ma zoben idanuwa. Kyam yake kallonsa, yana fitar da ruwan hawaye. Abun mamaki sosai ke akwai a cikin lamarin nan, ta yadda mutum mahaukaci kamar Annur, kuma ya san sai Maryama ta fita, sannan ya jawo ma'ajiyarta, ya ɗauko wata ajiya da ta yi. Abin da ya kasance yana aikatawa kenan tun daga ranar da ta fara exams, kullum sai ya buɗe wannan zoben ya kalla, har ma abun ya zame masa jiki. Ya jima a haka, kafin ya nannaɗe zoben kamar yadda yake a baya, ya miyar inda ya ɗauko sannan ya rufe drowar. Ban-ɗakin ya nufa kai tsaye, ya yi brush ɗinsa, sannan ya yi alwalla ya fito. Sadda Maryama ta dawo ana kiran sallar azahar, da farin-ciki ya tarbe ta. Sallah suka yi sannan cikin ujila ta nufi ɗora girki, jellof ɗin macaroni. Ta koma ta masa wanka ya shirya cikin baƙar jallabiya, sannan ita ma ta yi nata wankan, ta saka ƙananan kaya. Knocking ta ji ana yi, daga kitchen ta fito tana tambayar waye, muryar Jiddah ta ji ya sa ta gaggauta isa bakin ƙofar ta buɗe mata. Rungumar junansu suka yi cike da farin-ciki, sannan suka ƙarisa kan 2 seater suka zauna. "Ƙawata amarya." Jiddah ta faɗa tana murmushi. "Mara kirki, ai saura kaɗan in yi fushi da ke." "A yi min afwa, ai ga ni na zo. Ɗazu ina ta kiranki ma ba ki ɗauka ba, dama in faɗa miki zan zo yau." Maryama ta jawo wayarta daga kan hannun kujera, ta duba, ta ce, "Wallahi na yi exam ne yau. Dawowata gidan ma kenan, ko girki ma yanzu na ɗora shi. Kuma ban duba wayar ba." "Wannan jarabawa dai ba ta kyauta miki ba gaskiya. Daga amarci kuma sai jarabawa?" "To ya za a yi Jiddah. Sai haƙuri. Ai da yake ma next week zan gama insha Allah." "To Allah ya nuna mana." Daga nan Maryama ta koma kitchen, ta samu har girkin nata ya dahu. Sauran pepper soup ta fiddo daga fridge ta yi warming ɗinsa, sannan ta zuba ma Annur nashi daban, sai kuma ta zuba musu a tray ita da Jiddah. A ɗakinsa ta fara kai masa da drink, sannan ta ɗauko nasu ita da Jiddah suka ci. Bayan sun gama duka ne Jiddah ta hau labarta ma Maryama tarayyarsu da Deedah. Tun daga farko har ƙarshe ta sanar da ita, da kuma manya da suka shiga maganar. Maryama ta yi murmushi sosai, sannan ta ce, "Ka ji masoyan asali. Ni kam ai ba ni da labari. Kuma Hammad bai zo ba na san da na ji a bakinsa." Duka fa jiya ne Abbanku da Dadynsa suka je wurin Abbana, suka yi magana wai next week ma za a kawo kayan saka rana. To ni dai Maryama sai nake ga kamar an yi azarɓaɓi, ba wani jimawa muka yi ba amma har a fara batun saka rana?" Maryama ta kai mata dukan wasa, ta ce, "Ke banza ce wannan yarinyar. Mene ne abun azarɓaɓin a ciki? Insha Allahu akwai alkhairi a ciki. Mu kam a sha shagalin biki mu cashe." Haka suka sha yinin ranar cikin nishaɗi, sai misalin shida na yamma sannan Deedah ya zo ɗaukar ta. Cikin farin-ciki suka gaisa da Maryama, tamkar babu wani abu da ya taɓa faruwa a tsakaninsu. Bai wani jima ba Jiddah ta tashi suka tafi. Bayan wasu kwanaki *** *Tab! Ni kaina na sha mamakin tsayin shafin nan fa. Kusan yini uku na ɗauka ina aiki a kansa. Dama na ɗaukar muku alƙawari cewa page 70 insha Allahu zan muku dogon shafi, to ga shi dai na yi a 67. Saura kuma idan kun ga guntu a 70 ku ce ban cika alƙawari ba🙄.* *Me za ku iya cewa game da abubuwan da suka faru a cikin shafin nan?* *Ina buƙatar comments ɗin ku sosaai, matuƙar na ga kadan, to gaskiya sai an yi kwanaki kafin a sake ji na.* *Godiya ga masoyina duka. Ina ƙaunarku fisabilillah.* Thanks all. Pinky durling💞 RAZ 2 [9/22, 8:13 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taɓa zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 6⃣8⃣ Wattpad: PrincessAmrah *** A gajiye ta gama gyare-gyaren gidan, ta dawo ɗaki cikin sanyin jiki, ta hunce sannan ta ɗaura towel. Daidai ta kama hanyar shiga ban-ɗakin ne ta ji wayarta na ƙara, ta dawo ta ɗauke ta daga bisa bakin gado. Ganin wanda ke kiranta ya sa cikin hanzari ta yi recieving, sallama ƙunshe a bakinta. "Good afternoon Doctor." Ta faɗa cike da girmamawa, har ɗan rusunawa take alamar girmamawa. "Kina lafiya?" Ya faɗa cikin sakin rai. "Lafiya ƙalau. Ya aiki?" "Aiki muna ta fama. Ya mai jikin nan?" "Mai jiki da sauƙi." Ya ɗan yi shiru, kafin ya ce, "Na kira na faɗa miki cewa ina Kano right now. Insha Allahu tomorrow I'll be on my way to Katsina." Sassanyar ajiyar zuciya ta sauke, ta ji daɗi sosai, ta ce, "Ok Doctor. Thank you very much. Insha Allahu gobe zan kira da yamma." Suka yi bankwana ta kashe wayar. Wankan ta nufa tana jin farin ciki lulluɓe da zuciyarta, har ma ba za ta iya misaltawa ba. Bayan ta fito ta yi shafa sama-sama ta saka riga da skirt na English wears. Ta fesa turare sannan ta fita falo. A kan doguwar kujerar ta same shi barci ya ɗauke shi, ga kuma TV a kunne. Gyaɗa kanta ta yi cikin tausayi, a bayyane ta furta, "Ashe daga kallo barci ya ɗauke ka." Sannan ta kashe tv ɗin. Remote ɗin AC ta ɗauka ta rage ƙarfinta saboda ɗan makurewar da ta ga ya yi. Ta jawo wayarta da ke kusa da shi ajje, ta latso kiran Jiddah. Bayan Jiddah ta ɗauka ne suka gaisa, take ce mata, "Matar Yaya albishirinki." "Goro." Jiddah ta faɗa a ɗaya ɓangaren. "Fari ko ja?" "Ke wuya ta da ke jan ran masifa idan za ki faɗa wa mutum abu. To dilla can fari." "Ke kuma wuyata da ke masifa. To likitan nan da na ba ki labarinshi kwanaki. Yanzu ba da jimawar nan ba ya kira ni da kansa, yake ce min yana Kano, wai gobe idan Allah ya kai mu zai zo neman abokin nashi, sai mu haɗu da Yah Noor ɗin." Cikin jin daɗi Jiddah ta ce, "Ahh! To Alhamdulillah! Abu ya yi kyau sosai wallahi. Allah ya tabbatar mana da alkhairi. Allah sa haɗuwar ta zama alkhairi." "Ameen ya Allah, Jiddah. Na gode ƙwarai ki gaida Mami." "Za ta ji. Ki gaishe da mara lafiyan." Tana gama wayar tana jin knocking, ƙananan kaya ne a jikinta, hakan ya sa ta furta, "Ina zuwa." Sannan ta wuce ɗakinta da azama ta sako hijabi ta fito. "Waye?" Ta faɗa a hankali. "Ni ce." Muryar Umman Amrah ta daki kunnuwanta. Da hanzari ta buɗe fuskarta ƙunshe da murmushi. Tsayawa ta yi cak! Ganin Annur kwance a doguwar kujera yana barci. Cikin ɗan jin nauyi ta juyar da kanta. Fahimtar hakan da Maryama ta yi ya sa ta ce, "Ummah mu je ɗakina." Ta kama hannun Ummar. Suna isa ta zauna a kan sofa, tana faɗin, "Sannu da zuwa Umma. Ya gida ya kuma Mallam? Ya gama warwarewa sosai dai ko?" "Alhamdulillah. Ya warke sosai ma. Ya na same ku?" "Lafiya ƙalau Umma." Maryama ta faɗa fara'a ƙunshe a bisa fuskarta. Umma ta ce, "Jiya ai na yi waya da Maman Hammad. Ita ke ce min wai kin faɗa mata ba ki ji daɗi ba har yanzu ban zo ba. Na ga rashin kamatuwar zuwa gidan yara ne shi ya sa ban zo ba." "Haba dai Umma! Meye a ciki don kin zo inda nake? Nake ga kamar an zama ɗaya ai." "Duk da haka dai Maryam ai bai kamata ba. Yanzun ma dai abin da ya sa na daure na zo saboda wani abu da na tuno game da Amrah, nake son faɗi a gaban Annur ɗin, wata ƙila ya iya tunowa da wani abu. To kuma ga shi ma na samu yana barci, ban kuma zo da nufin doguwar zama ba gaskiya." "A'a fa Umma. Gaskiya dole ki tsaya ki ci abinci, kafin nan ma na tabbatar ya tashi daga barcin." Murmushi Umma ta yi, ta ce, "To zaman me zan yita yi a gidan nan Maryam?" Maryama ba ta ko tsaya saurarar Umma ba ta wuce kitchen. Coconut rice da vegetable sauce ce ta zubo mata daban-daban ta ɗora a tray da drinks ta kawo mata. Sosai take hidima da Umma, tamkar tata mahaifiyar. Bayan ta gama duka ta dawo ta zauna, ta ce da Umma ta ci don Allah, kuma da yawa take son ta ci. Babu musu Umma ta fara cin abincin, ba ta wani ci da yawa ba ta ajje cewa ta ƙoshi. Duk yadda Maryama ta so ta ƙara amma ta ce ta ƙoshi, don haka ta kwashe kayan sannan ta gyaggyara wurin. "Maryam tashi zan yi in tafi fa, da alama dai ba yanzu zai tashi ba. Ki ga fa har an fara kiran sallar la'asar." "Amma dai ban ji daɗi ba Umma. Da alama dai zan kira Abba a aiko da mota in zo har gida da shi, tunda dai ya ƙi tashi daga barcin yanzu." "Zan daure ko nan da kwana uku ne in dawo. Kar ki fitar da shi gaskiya, gudun samun matsala." "To shi kenan Umma. Na gode ƙwarai." Daidai Ummar ta tashi ita kuma Maryama ta jawo ledoji guda biyu, ta saka turaren touch me guda ɗaya, sai kuma freshner mai ƙamshi guda. Bayan sun fita daga ɗakin kuma ta je kitchen ta ƙarisa juye ma Umma cin-cin da dublan ɗin da suka rage a gudar ledar. Ta fito. Da ƙyar ta samu Umma ta karɓi kyautar tata, ta buɗe ƙofa za ta fita kenan Annur ya tashi. Juyowa suka yi a tare suka yi tozali da juna, da murmushi Maryama ta ce, "Umma kin ga ya tashi ma." Suka sake dawowa falon. Bayan sun zauna, Maryama ta kalle shi da murmushi ta ce, "Yah Noor ga Umman Amrah fa." Ya kalli Umma. Bai ce komai ba sai murmushi da ya saki yana kallon ta. Umma ta ce, "Sannu Annur. Ya ƙarfin jiki? Ka ji sauƙi ko?" Ya ɗaga mata kai. "To Allah ya ƙara sauƙi." Shiru ya biyo baya. "Zan yi fitsari." Ya faɗa ma Maryama yana kallon ta. Kama shi ta yi ya miƙe, a haka suka isa toilet ɗin ya yi fitsari sannan ta masa alwalla suka dawo falon. "Umma ko za ki faɗa masa maganar?" "To Maryam." Ta miyar da kallon ta ga Annur. Sai da ta sauke ajiyar zuciya sannan ta ce, "Akwai wani labari da Amrah ta taɓa faɗa maka a gabana. Cewa wai tana ganin wani bawan Allah mai irin kamanninka. Za ka iya tunowa?" Shiru ya yi yana bin ta da kallo. Ta ci gaba, "Ka san sai na kwaɓe ta da zancen, saboda tun farko ban so ta faɗa maka ba, gudun zargi." Nan ma dai ya yi shiru. "A ranar da wannan abun ya faru, ka kawo ma Amrah wani zoben zinari mai matuƙar kyau, har ka ce tsarabarta ce da Kawunka ya siyo mata daga Dubai da ya je. Idan za ka iya tunawa, Amrah ba ta karɓi wannan kyautar ba, ta ce ka miyar ka ajje har sai ranar da aka ɗaura muku aure sannan ka ba ta. A lokacin sosai ka nunar da rashin jin daɗinka, ta yadda za ka kawo mata kyauta daga wurin kawunka amma ta ƙi karɓa, har ka sako ni a cikin zancen. Ka tuna?" Bai ce komai ba, kamar yadda ta yi tsammani dama ba zai ce ɗin ba. Ta ce, "Ni ma da kaina na goyi bayan kar ta karɓi wannan kyautar, saboda zoben ba ƙaramin zobe ba ne, irin wannan kyautar abin da ya kamata a bari har sai an yi aure sannan a yi ta. A bayyane ka nunar da rashin jin daɗinka, har ka yi fushi da Amrah, ko in ce da mu duka baki ɗaya. Ka ɗauki tsawon lokaci ba ka dawo ba, sai dai muka ji ka shiru, har a waya ba a jin ka, ashe ba ka da lafiya ne. Cikin tashin hankali muka nufi gidanku, Mahaifiyarka ke faɗa min ai kana ma asibiti an kwantar da kai, amma mu jira ita ma a lokacin za ta tafi, sai mu je tare. Tare muka tafi da ita har da Amrah, mun same ka sosai ka ji jiki. Sai a ƙarshe nake jin labari a wurin Amrah, kasantuwar ba ta ɓoye min komai, tunda ba wata ƴar uwa mace gare ta ba, kuma ba tarin ƙawaye ke gare ta ba. Dole ni kaɗai take kawo wa maganarta, kamar yadda ni ma ita nake nufa da kowacce irin matsala tawa. Take ce min wai saɓanin da kuka samu ne dalilin ciwonsa. SHI NE SILAH! Na yi mamaki sosai, ta dalilin zobe har wani abu ya gitta tsakaninku, har a ƙarshe ka kwanta asibiti? Mahaifinta ya so mu karɓi kyautar zoben, sai dai fa ni ina tsoro, tsoron danginka nake, su Islam ba su da kirki. Bai kamata mu karɓi wannan kyautar tun a lokacin ba. Tun bayan ka ji sauƙi kuka daidaita, a nan kuma Amrah ke faɗa min wai ka miyar da zoben ga kawun naka, ka ce ya ajje maka har sai sadda aka tashi aurenka, sannan ya damƙa shi ga mai shi, wato Amrah. Zobe dai haƙƙin Amrah ne, Annur. Amma na sadaukar da shi gare ka, ka karɓo shi daga wurin kawun naka duk sadda ka samu lafiya, ka ajje shi ko ka kayutar, duk yadda ya maka, mun bar maka." Ta dakata daga nan, tana kallon yadda idanuwansa suka yi taf da ƙwalla. Maryama ba ta yi mamakin jin kalaman da suka fito daga bakin Umman Amrah ba. Domin kuwa dama ta riya a ranta, ta tabbatar cewa wannan zoben na Amrah ne, saboda yadda ta ga Annur ya ɗauke sa da muhimmanci. A yadda ta ƙara jin tausayin Amrah, ji ta yi ina ma Amrar za ta dawo a yanzu. Wallahi da ta mallaka mata Annur. Da ta nemi rabuwa da shi ta bar masoyan su cika burin rayuwarsu, burin zukatansu. Sai a yanzu ne take ƙara tabbatarwa, cewa Annur da Amrah ya dace. Tamkar jininsu na tafiya a tare ne. Kansa ya ɗora bisa hannun kujera yana kuka, kuka mara sauti sai dai shessheƙarsa kawai da ake ji. A hankali Maryama ta isa gare shi, ta tallabo kanshi ta ɗora a cinyarta, ta saka hannunta na dama ta hau share masa ƙwallar, tana faɗin, "To miye ne abun kukan kuma? Ka yi shiru, ka ji?" Ta fuskanci Umma ta ce, "Na matuƙar jin daɗin sirrin zoben nan Umma. Na jima ina son sanin wani abu dangane da shi, sai dai jikina ya ba ni dama ya danganci Amrah. Yanzu haka zoben yana wurina..." Ta ba Umma labarin duk abin da ya faru. Ta ƙare da cewa, "Kuma tun daga sadda Yah Noor ya ga wannan zoben na tabbatar da zoben ko ƙaƙa ne ma ya yi silar samuwar sauƙinsa. Tun daga ranar yake yin abubuwa na ban mamaki. Wanda har gani nake kamar ma ya warke ne. To kuma sai idan ya yi wani abun ne nake daɗa tabbatar da cewa bai warke ɗin ba, ya dai samu sauƙi sosai." Umma ta yi hamdala ga Allah sannan ta miƙe cewa za ta tafi. Har gate Maryama ta raka ta sannan ta dawo ta same shi. * "To Alhamdulillah! Sauƙi ya samu sosai. Yanzu ma likitan ya bar nan, ya tabbatar min da cewa Annur ya samu sauƙi. Ya ma ba shi sallama, gobe idan Allah ya kai mu za mu dawo gida Nigeria." Daga can ɗaya ɓangaren Momy ta sauke nannauyar ajiyar zuciya, ta ce, "Wannan zancen ya min daɗi ƙwarai Alhaji. Allah ya ba shi lafiya ya kyauta gaba. Sannan Alhaji don Allah ka masa nasiha sosai kafin ku dawo ni ma na masa tawa." "Abin da nake da shirin aikatawa kenan kika kira ni Suhailah. Zan mishi sosai." "To shi kenan sai anjima. Allah ya dawo mana da ku lafiya." "Ameen." Ya faɗa haɗe da tsinke wayar ya fuskanci Sans da ke jingine da kan gado. "Annur!" Ya ɗago kansa ya kalli Dady. "Ina so ka faɗa min tsakaninka da Allah a kan tambayar da zan yi maka." Gabansa ne ya ji ya yi matsanancin faɗuwa. Cikin rawar murya ya ce, "To Dady." Dady ya ce, "Annur me ke damun ka?" Shiru ya yi bai ce komai ba, har ya sake jin muryar Dadyn ya ce, "Na tabbatar da cewa kana da damuwa. Ba zai yiu ba ka da damuwar komai ba ka yi attempting kashe kanka. Don Allah ka faɗa min abin da yake damun ka. Na maka alƙawarin warware maka damuwarka, da ƙarfin mulkin Allah." "Dady..." Ya yi shiru sanadiyyar kukan da ya zo masa. "Dady tabbas ina da damuwa, sai dai ba irin wacce za ta faɗu ba." Cikin mamaki Dady ya ce, "Annur dama akwai damuwar da ba za ta faɗu ba?" Kai Sans ya ɗaga masa, yana mai share ƙwallarsa. "Waye ni a gare ka?" "Babana." "Babanka kawai?" Sai da ya ɗan jinjina kalmar kafin ya ce, "Mahaifi." "Good. To Annur idan ba ka tinkare ni da matsalarka ba waye za ka tinkara da ita ya warware maka? Me ya sa ka yi yunƙurin kashe kanka? Anya kuwa ka san hukuncin wanda ya kashe kansa?" Da sauri Sans ya ce, "Na sani Dady." "Mene ne to?" Dadyn ya tambaye sa. "Ya mutu kafiri. Ɗan wuta ne." "To ka san da hakan Annur me ya sa za ka jefa kanka ga halaka da iliminka? Shin har akwai damuwar duniya da ta fi ta lahira tsanani? Haba Annur! Wane dalili zai sa kana ji kana gani ka luma wa cikinka wuƙa? Yanzu inda a ce da ka luma ɗin ka mutu, me za ka faɗa wa mahaliccinka? Za ka ce masa damuwar duniya ce ta maka yawa har ka kashe kanka?" Gyaɗa kansa ya yi Sans. "Ehen...to ina sauraren ka. Mece ce matsalarka?" "Dady baki ɗaya duniyar ce ta juya min baya. Farin-ciki na ya kau. Damuwa ta tattaru ta lulluɓe min zuciya. Ƙunci ya min yawa. Na rasa yadda zan yi in samu assauci, shi ya sa na yanke hukuncin kashe kaina." Dady ya numfasa, sannan ya ce, "To na ji. Amma mene ne sila?" "Dady babbar silar ce ke da nauyin faɗe. Ƙaramar kuma rasa aminina Farouk da na yi ne." "Na san wannan na ciki Annur. Amma dai ina da buƙatar sanin babbar damuwar, komai girmanta." Ƙara ƙarfafa kukan nasa ya yi, ya ce, "Ka yi haƙuri ka yafe min Dady. Ni mai manyan laifuffuka ne. Amma don Allah ba don hali na ba, ka zama mai yafiya a gare ni, sannan kuma kar ka tsananta binciken koma miye. Na maka alƙawarin ba zan ƙara yunƙurin kashe kaina ba. Ina so komai daren daɗewa, wani abu ya taso game da ni kar ka guje ni Dady, kar ka juya min baya..." Jawo shi Dady ya yi a jikinsa yana ɗan bubbuga bayansa cikin rarrashi. "Na maka alƙawarin ba zan taɓa juya maka baya ba Annur, duk wuya duk rintsi. Kai fa ɗana ne na cikina. Ka taɓa ganin inda hannunka ya ruɓe ka yanke shi ka yar? Ka kwantar da hankalinka. Allah ya ƙara maka lafiya." Sosai ya ji daɗi Sans. Sai dai a zuciyarsa tausayin Dady yake. Ta yadda ya yarda da shi, ya ɗauke shi matsayin ɗan da ya haifa da cikinsa, amma kuma ba hakan ba ne. * Cike da mamaki yake kallon ta a falon. Fuskarsa a sake ya ƙariso gabanta ya zauna. Sannu da zuwa ta masa cikin faraa. "Ai yau mamaki kawai nake Yamairah a falo. Hala dai ke ma kin fara gajiya da zaman ɗakin ne?" Murmushi ta sakar masa. "Ba gajiya na fara yi ba. Yesmeen ta yi ɓarna a ɗakin ne na tura mai aiki ta gyara. An dawo lafiya?" "Alhamdulillah. Tunda dai bakya komai kuwa tashi za ki yi mu fita?" "Zuwa ina?" Ta gaggauta tambayarsa. Don ita kam ba son yawan fita take ba. "Wurin yankan kai zan kai ki." Suka yi dariya su duka. "Nan cikin unguwar nan ne babu nisa. Mamaki zan ba ki ne, na aurar da ɗana ba ki sani ba." Murmushi ta yi, "Ok bari in sako hijab." Ta nufi ɗakinta. A lokacin har mai aikin ta gama gyaran ɗakin. Bayan ta sako hijabi ta ɗauro niƙab ɗinta kamar yadda ta saba idan za su fita. Ta ɗauko wayarta sannan ta cicciɓo Yesmeen da ta yi barci tun sadda ta gama ɓarna ta sauko ƙasa. Cikin Corolla S suka tafi, duk da dai cewa babu nisa amma a ƙafa za a wahala sosai. Sadda suka isa gidan horn ya yi mai gadin ya leƙo ya ga ko waye. Ɗaga masa hannu ya yi alamar gaisuwa sannan ya wage masa gate ɗin gidan suka shigo da motar. Sadda suka fito daga cikin motar har Yesmeen ta tashi. Da ƙafafuwanta ta taka suka ƙarisa ciki. Duk da Yamairah na son tambayar mijin nata ko me suka zo yi a nan? Sai ba ta furta ba. Ta zuba masa idanuwa kawai suka isa ciki. A falo suka samu Maryama tana yankan ƙumba. Annur kuma tunda suka gama sallah sai bai fito ba. Saboda zallar damuwar labarin da Ummar Amrah ta tado masa da shi. Yana ji ne kamar komai ya dawo masa sabo. Da murna ta miƙe tsaye tana musu sannu da zuwa, haɗe da yi musu iso suka ƙarisa shigowa cikin falon. Sarai ta tuna da ƴar yarinyar, wannan shagwaɓaɓɓiyar ce da suka tayar a falo ranar da suka je gidan. "Sannun ku da zuwa Uncle. Sannu Aunty." Ta kama hannun Yesmeen. Noƙe kafaɗa ta yi haɗe da janye hannunta ta koma wurin Babanta. Gaisawa suka yi, a zuciyarta tana jinjina kyawu irin na Yamairah. Dole ne wannan za ta zama ƴar kulle, dole kuma ta ringa saka niƙab. Saboda sadda suka shigo falon ba ta ɗage niƙabin ba har sai da ta zauna. "Kawu ya gida?" "Gida alhamdulillahi, Maryama. Kuka ji ni shiru ban dawo ba ko?" Ta ɗaga kanta da faɗin "Babu komai ai. Na tabbata uzururruka ne." "Wallahi kuwa. Yayana ya je India ne, so kuma ina ɗan kula masa da wasu abubuwan nashi, ni ma kuma ga nawa, sai abun ya taru ya haɗe min." "Allah sarki! Yarinya ya sunanki?" Ta faɗa tana murmushi. Yamairah ta ce, "Shereefa, amma Yesmeen ake kiranta da." "Allah sarki! Sannun ku da zuwa." Ta miƙe haɗe da nufar kitchen. Blue cocktail ta ɗoro a tray da cups guda biyu. Sai kuma bobo saboda Yesmeen. Ta kawo ta ajje a gabansu suna mata sannu. Alhaji Marwan ya ce, "Wai ina mutumin ne?" "Yana ɗaki kawu, tunda muka yi sallah bai fito ba. Bari in kira shi." Ta miƙe haɗe da nufar ɗakin. Fitowa suka yi tana gaba yana biye da ita, kan Yamaira duƙe a ƙasa tana zuba wa mai gidanta lemu. Suna isowa Yamaira na ɗago kanta. Karaf suka haɗa ido da Annur da ke ta famar yaƙe bayan ya zauna. Ido buɗe take kallonsa, har cofin hannunta na glass ya faɗi ƙasa, saboda bisa kafet ne ma ya sa bai fashe ba. Sai dai lemun ya zube, kwalbar lemun ma ta faɗi ƙasa duka ta zirare. Da mamaki suke kallon ta su ɗin ma. Alhaji Marwan ya ce, "Lafiya?" Ya miyar da idonshi ga Annur da ta ƙura ma idanuwa. Shiru ya ji ba ta ce masa komai ba. Ya maimaita tambayarta amma ba ta ko san yana yi ba. Hannuwansa ya sa a daidai fuskarta ya tafa da ƙarfi, ta firgita tana nuna sa da ƴar yatsa. Hakan bai mata ba ta miƙe tsaye ta isa gabanshi. Hannunta ta sa ta tattaɓa goshinsa a hankali, tunaninta ko mafarki take. A ganinta wannan abu ne da ba zai taɓa yiuwa ba. Miƙewar ya yi shi ma Alhaji Marwan cike da mamaki ya ƙariso inda suke. "Yamaira me ke faruwa kike taɓa shi? Kin san shi ne? Please talk." Kuka ta fasa mai ƙarfi. Ta rinƙa gyaɗa kanta, tana faɗin, "Yaya Salman! Kai ne ko ba kai ba ne? Me ya dawo da kai nan? Dama kana raye?" Da ƙarfi ta faɗi ta zube a wurin. Alhaji Marwan da Maryama suka yi kanta. Annur kam kallon mamaki kawai yake bin ta da shi. *** *Sannunmu sannunmu da jimirin karatu. Kun ga yadda sannu a hankali muka fara kai gangara ko.* *Hirar Sans da Dady fa ta ɗan birge ni, a wani ɓangaren kuma ga tausayi. Wato dai na fahimci cewa Sans ya nadama, sai dai yana gudun ya tona asiri ne kar su kore shi daga gidansu, ya rasa tudun dafawa. Ko ya abun zai kasance duk ranar da wannan rufaffen asirin ya buɗu?* *Su Yamaira an ga ɗan uwa an sume🤣 to idan ta farfaɗo mene zai faru?* *Abubuwan fa akwai rikitarwa😀 amma sannu a hankali duk za a warware mana komai, tunda ga shi an fara warwarewar ma.* *AREWA NOVELS GROUP ba na cikin group ɗin amma saƙon gaisuwa da jinjinarku ya iso gare ni. Amrah na godiya sosai. Allah ya bar zumunci.* *Comments ɗin ku na last page sun min daɗi sosai. Ina fatar zan samu fin hakan a wannan.* *Na gaishe ku masu mutunci. Ba laifi aikinku yana kyau, amma last page duk ƙoƙarin da na muku na dogon shafi sai ban ga an kankaro shi yadda ya dace ba. Fatar za ku gyara. Ku rabu da waƴancan masu hancin yalo da kabewar, su dama sun saba cin amana. A kyautata musu amma su yi ha'inci.🙄 ehh da ku nake. Wanda ke min laɓe a littafi.* Thanks all. Pinky durling💞 RAZ 2 [9/24, 6:57 AM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taɓa zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 6⃣9⃣ Wattpad: PrincessAmrah *** Kakkaɓe-kakkaɓen ɗakin suke su duka biyun, suna yi suna ƴan ɗage-ɗagen komai saboda su samu gyara shi yadda ya kamata. Sai da suka ƙarisa duka shara kawai ta rage Hanan ta ce ma Janan, "Janan don Allah ko za ki taimaka ki ƙarisa sharar ɗakin nan, please? Cikina ke ɗan min ciwo wallahi." Kallon banza ta bi Hanan ɗin da shi. Ta ce, "Malama in kina zama mu ƙarisa aikin nan ma ki zauna. Don ƙafarki ƙafata." Dama jikinta ya ba ta sam Janan ba za ta mata wannan alfarmar ba, saboda tun dama can Janan maƙyuyaciya ce. Sai ta ɗaure fuskarta, ta ce, "To don Allah Janan kar ki share ɗin, tunda ke ba ki san arziƙi ba. Ciwo dai ne ya san gidan kowa." Ta buga tsaki haɗe da barin ɗakin. Tsakin ta yi ita ma Janan, ta ce, "Mai wayon banza. To ba zan share ɗin ba. Ni bari ma in yi bincike ko Allah zai haɗa ni da abin da raina zai so, tunda Uncle Noor akwai shi da iya ajiyar abon arziƙi." Rawar kai gare ta dama Janan. Bambancinta da Hanan kenan. Ko sadda suka taɓa zuwa tare da Annur ɗin daga Cyprus ita Hanan ce ta gwada wa Amrah soyayya. Janan kuwa ta biye su Islam suka tsani Amrar tare. Binciken kuwa ta hau yi, jawo wancan buɗe wancan haka ta rinƙa yi. Banda tsofaffin shisha babu abinda ta rinƙa gani, sai tarin flavors linkim. Tsaki ta rinƙa yi tana sake buɗowa, har Allah ya haɗa ta da diary ɗin Sans. Ɗauko shi ta yi ta taɓe fuska, "I must read this. Sai na jiyo sirrin Uncle Noor. Ƙila ma a ciki in san dalilinsa na ƙin yin aure har yanzu." Sai kuma ta sake taɓa baki, ta ce, "Hala ma dai labarin wannan mai sickler ɗin da ta rasu ne a ciki, don na san halinsa shi dai Amrah kawai. Ko ma dai miye I must read it." Ta ajiye a gefe guda, sannan ta ci gaba da bincikenta. Idan handky ta gani da ya birge ta sai ta ɗauka. Tana gamawa ta harhaɗa komai yadda yake ta miyar, sannan ta tattara abubuwan da take so ɗin ta saka cikin wata farar ledar shoping da ta samu, har diary ɗin ma. "Ai kam komai dare yau sai na karanta diary ɗin nan. Don ni ba na aikata abin da ya dace kurum, har wanda bai dace ɗin ba ma yi nake." Ta gatsine fuska tamkar tana yi da wani ne. Ba ta tsaya sharar ɗakin ba kawai ta fice daga ɗakin, da ledar karikitan da ta ɗauko ɗin a hannunta. Saɗaf-saɗaf ta rinƙa yi don kar a gan ta a tambayi abin da ke hannunta. Ji ta yi an ce, "Sarkin ƙiriniya tabbas akwai abin da kika yi, wannan sanɗon da kike yi ba a banza ba." Zabura ta yi alamar jin tsoro, ta yi saurin tattaro dukkanin nutsuwarta, fuskarta ƙunshe da dariyar yaƙe ta ce, "Babu fa komai Momy. Wani tiƙeƙen ƙadangare ne fa na gani shi ne nake laɓe don kar ya kama ni." Bayyanannen tsaki Momy ta yi. "Ba ki da gaskiya da ganin fuskarki. Faɗa min gaskiya Ussaina. Miye a cikin ledar nan?" "Uhm...Momy..." Ta kama susar ƙeya. Muryar Hanan ta ji ta ce, "Shara na ce mata ta yi ta ƙi yi Momy. Kuma na faɗa mata fa ba ni da lafiya cikina na ciwo. Na koma in ga ta yi sharar ko ba ta yi ba? Na tarar ta jawo lakokin Uncle Noor sai bincike take masa. Idan ƙarya nake kuma ta buɗe wannan ledar ta hannunta a gani." Harara take buga ma Hanan amma hakan bai sa ta yi shiru ba har sai da ta dire. "Wallahi mutum magulmaci dai bai yi ba. Yanzu sharri za ki min a wurin Momy?" "Ba wani sharri. Idan ba tsoro ba ki buɗe ledar a ga." "Ba zan buɗe ɗin ba. Maganin zafi ne fa na karɓo daga wurin Mallam Ya'ulle." Dariya ta ba Momy. Ta ce, "Allah dai ya shirye ki. In ma dai wani abu kika kwaso wa kawun naki kwa haɗe da shi ne. Kun ga ni dai, har sha ɗaya ta yi, ku hanzarta nufar kitchen, ƙarfe ɗaya jirginsu zai sauka Kano. Dreba ma ya tafi ɗauko su." "Duk baƙin-cikin mutum dai..." Ta ma Hanan gwaliyo haɗe da nufar ɗaki. Gyaɗa kai Hanan da Momy suka yi. Ta ce, "Momy bari in daure in sharo masa ɗakin, don na tabbata ba ta share shi ba." Ta nufi fita zuwa ɗakin nasa. Janan kuwa wardrobe ta buɗe can tsakiyar kaya ta saka ledar, bayan ta fiddo diary ta saka a ƙarƙashin pillow ɗinta. Fitowa ta yi ta nufi kitchen. Tafashen nama ta ɗora ta zuba kayan ƙamshi da albasa. Ta taɓe baki ta ce, "Na yi iya yi na. Wallahi fruits kawai zan yanka na gama. Ba zan iya ba." Ta murguɗa bakinta, ta fiddo fruits ɗin daga cikin babbar ledar da aka siyo su, ta hau aikin yanka. Tana cikin yi Hanan ta shigo, Momy biye da ita. "Janan what are you doing fisabilillah? Miye na fara yankan fruits bayan babu abin da aka yi?" "Gaskiya matar nan kina da damuwa. Idan ban yi ba ki ce na cika ƙyuya. Ga shi ina yi kuma ban yi daidai ba. Gaskiya dai Momy ki shiga tsakanina da Hanan. Ta cika ƙorafi da mitar tsiya." Murmushi kawai Momy ke yi. Sosai lamarinsu ke ba ta dariya. Kamar mage da ɓera haka suke, su yi faɗa su shirya. "Ga tafasar nama can na ɗora. Shi kaɗai na gani ban san kuma me za a ɗora ba." "Aikin kenan." Hanan ta faɗa bayan ta isa ta buɗe tukunyar. Ruwan zafi ta ɗora a makimanciyar tukunya, sannan ta fiddo kaza mai ƙanƙara daga cikin freezer. Ta zuba mata kayan ƙamshi da su maggi da albasa. Nan take aiki ya tashi. Bayan ruwan ya tafasa ta zuba shinkafa da vegetables, kazar kuma pepper chicken ne dama za ta yi da ita. "Malama tafashen namanki ya yi fa tun ɗazu har ruwa ya tsane. Ko blending cefanen ma ba ki yi ba, kin dage ma aikin fruit salad tun ɗazu ya ƙi ci ya ƙi cinyewa." "Ke ni fa ba wata miya da zan yi. Kin dai samu na rage miki aiki ne. Kina ganin har yankewa na yi wurin peeling kankana." Ta kama yarfar hannunta. Gyaɗa kai Hanan ta yi. Duk da cikin nata bai daina ciwo ba, amma ta samu sassauci. A hakan ta ci gaba da aiki, ta gyara cefanen ta markaɗa a blender, ta soya naman sannan ta zuba cefanen a ciki. Cikin ƙanƙanin lokaci miyar ta hau turbar dahuwa. Ita kuwa Janan ta gama fruit salad ta yi ceiling da cling film ta saka a fridge. "Yanzu tafiya za ki yi Janan ki bar ni da uban aikin nan saboda Allah?" "Tambaya ma kike? Malama ki gama mana girki kawai mu kwasa." Ta mata gwalo da gudu ta bar kitchen ɗin. Dariya Hanan ta yi, "Allah ya shirya min ke Janan." Ta ci gaba da aikinta. * "Bai kamata ki tasa mu gaba kina sharar kuka ba Yamaira. Yamma ke yi fa, magrib ake neman yi. Tun bayan da kika farfaɗo nake fama da ke ki faɗa min damuwarki amma kin ƙi. Sai famar zubar da ƙwalla kike yi." Sai a sannan cikin kuka ta iya buɗar bakinta ta ce, "Kukan da nake yi da biyu; farin-ciki da kuma baƙin-ciki." Duk suka kalle ta cikin mamaki. Ita kanta Maryama mamakin Yamaira take, yadda take kuka haiƙan, ga kuma wani suna da ta ambaci Annur da shi. "Ina jin ki Yamaira, please talk." Ta share ƙwallarta. Wata sabuwar ƙwallar ce ta ƙara saukowa, ta ce, "Ka san komai game da ni Dadyn Yesmeen, duk abin da ya faru a rayuwata ka san shi. Ka kuma san yayana Salman da na faɗa maka tun bayan rabuwarmu da shi, ya je nema mana abincin da za mu ci ni da Aunty, ba mu sake ganinsa ba har sadda aka zo aka tafi da mu. To wannan bawan Allah'n na zaune shi ne Yayana Salman! Wallahi shi ne!" Kuka ya kuma cin ƙarfinta. Kansa ya ɗaga Alhaji Marwan. Ya ce, "Ehh ƙwarai na san da zancen. Amma ya aka yi ya zama Salman? Kodai kin manta fuskar tasa ne?" "Haba Dadyn Yesmeen! Ko ina manta fuskar kowa ta ya zan iya mantawa da ta gudan jinina? Babu ko tantama yayana ne wannan. Salman." Cikin mamaki da son jin zancen Maryama ta ce, "Ban san komai ba. Please ko za ki faɗa min? Ta yiu akwai wani taimako da zan iya ba ki." Ta kuma share kumatunta. Ta ce, "Sunana Yamaira..." Ta kwashe komai, tun daga farko har ƙarshe ta sanar da Maryama. A ƙarshe ta ce, "Bayan wannan mutanen sun tafi da mu, suka ɗaure mana fuskoki ba tare da mun san inda suka nufa da mu ba. Sai da muka isa wani ƙasurgumin daji sannan suka buɗe mana fuskokin namu, suka shigar da mu wani babban gida. A nan muka ga jerin mata birjik, wasunsu a cikin damuwa, wasu kuwa hankalinsu kwance suke hidimar gabansu. A wannan gidan muka ci gaba da zama, har tsawon wata ɗaya. Kwatsam cikin wani dare aka kawo ma ƴan ta'addar hari, sojoji da gwamnati ta turo, kuma suka gano daji da gidan da muke. Wannan sojojin ne suka fitar da mu, suka dawo da mu a cikin garin Maiduguri, cewa daga nan kowa ta nemo asalin gidansu ta koma. A nan tashin hankalina ya sake ninkuwa. Tuna ƙarar bomb ɗin da ya tashi a kangon da Aunty suke, da kuma fitar Yaya Salman bai dawo ba, ga uwa uba wayar ƙarshe da Yaya Salman ya yi da Abbu, ya ji sautin bindiga. Na ɗora hannuna a ka, na rasa uwar ubana. Damuwa ta bi ta dunƙule a cikin zuciyata. A nan inda nake tsaye na ji an taɓa ni, na juyo don ganin mai taɓa nin, sai na ga wata budurwa wacce ba za ta wuce sa'ar haihuwata ba. "Ki yi haƙuri kin ji. Dukkan tsanani yana tare da sauƙi." Ta faɗa cikin sassanyar muryarta. Na ce, "Ban san sadda nawa sauƙin zai zo ba." Ta murmusa, "Duk daren daɗewa zai zo gare ki." "Ina fatar hakan." Na faɗa cike da damuwa. "Zama a nan bai kamace ki ba a matsayinki na ƴa mace. Ki zo mu je gidanmu." Ban musa mata ba, saboda ko yawan magana ba na so. Na bi bayanta. Gaban wata danƙareriyar mota muka isa, aka buɗe mata baya, ta shiga haɗe da ba ni izinin shiga ni ma. Bayan mun isa gidansu ta sa na yi wanka, ta kawo min kayanta na saka. Ko da na gama shiryawa an jera min tarkacen abinci a gabana. Na yi mamakin yadda cikin daren nan aka iya haɗa liyafar abinci kamar wannan. Kaɗan na ci na ce na ƙoshi. Na kwanta barci. Nan fa damuwa ta sake ninkuwa, na nemi barci na rasa. Sai kuka da tunanin rayuwata da nake yi. A gidan su Ummi na ci gaba da rayuwa har tsawon watanni biyu, sannan ta ce min hutunta ya ƙare ita kam, za ta koma makaranta. A nan kuma hankalina ya kuma tashi. Na ce da ita zan koma Bama in binciki dangi da iyayena, ta ce ina, ai har yanzu akwai sauran tashin hankali a garin. Na kartake cewa sai na je, ta haɗa ni da mahaifanta. Da yake mutanen kirki ne, suka lallaɓa ni kan cewa in haƙura har a samu kwanciyar hankali a garin, duk da dai da sauƙi ba kamar da ba. Kalamansu masu daɗi suka siye min zuciya na haƙura. Kuma suka ce idan ina ga kamar zaman gidan ba zai min daɗi babu Ummi ba, sai in bi ta makaranta. Tare aka mana siyayyar dawowa duk da ni ba ɗaliba ba ce. A nan Al-Qalam University. Tare muka ci gaba da rayuwa, a lokacin da na cika watanni uku a garin ne Allah ya haɗa ni da Alhaji Marwan, har muka fara soyayya da shi. Sadda hutun first semester ya ƙare na su Ummi, muka koma gida hutu, na gabatar da Alhaji Marwan a matsayin wanda zan aura. Abii ya ce ya zo ya same shi su yi magana, tunda dai har na amince zan aure shi. Kin ji yadda komai ya faru. Kuma tun daga wannan lokacin muka koma Bama tare da Ummi da iyayenta da kuma Alhaji Marwan, muka tarar iyayena babu su, sai dai wasu daga cikin danginmu, wanda suka ɓuya. Amma mafi rinjaye duk an karkashe su basa raye. Sosai Abii ya yi bincike game da Alhaji Marwan, tamkar ƴarsa da ya haifa haka ya yi ɗawainiya da ni, ya aurar da ni ga Alhaji Marwan. Ga shi har da tukuicin Yesmeen, wacce na saka ma sunan mahaifiyata, Shereefah." Cike da mamaki Maryama ke kallon ta. Tausayinta take ji sosai, sai dai tsabar al'ajabi da labarin ya gama ba ta. Da ƙyar ta samu ta tattaro magana ta haɗa, ta ce, "To amma bara na miki wata tambaya Maman Yesmeen. Yaya Salman ɗin naku ƴan biyu ne asalinsa ko kuwa dai shi kaɗai ne aka haifa?" Yamaira ta ce, "Aunty ta faɗa mana wai twince ne, amma wancan ɗin ana haihuwarsa ya rasu..." Tun ba ta rufe baki ba Maryama ta miƙe tsaye. Sai yanzu hasashen nata ya tabbata. Kanta ta dafe, tana jin tunani kala da kala a cikin zuciyarta. Ta ma rasa abun yi, ganin komai take tamkar a mafarki. "Ta faru ta ƙare! An yi wa mai dame ɗaya sata." Ta furta tana fifita da tafukan hannayenta duka biyun, saboda wani irin gumi da ta ji yana tsattsafo mata. "Kenan dai Yah Noor ba su Momy ne suka haife shi ba?" Shi kanshi Alhaji Marwan zancen da yake kenan a zuciyarsa. Ya cire hular kansa yana fifita da ita. Dawowa ta yi ta zauna Maryama. Cikin kuka ta ce ma Yamaira, "Wannan ba shi ne ainahin Salman yayanki ba..." "Don't tell me rubbish! Ta ya za ki ce min wai ba yayana ba ne, bayan kuma ina a cikin hankalina?" "Duba shi da kyau Yamaira. Na tabbatar da dole koma ƙaƙa ne akwai abin da za a iya samu bambanci nasu. Sannan kuma wannan ma ba shi da hankali fa." Yunƙurin miƙewa zaune ta yi ta kasa. Maryama ta taimaka mata ta tashi zaunen, ta zuba ma Annur idanuwa. Da ƙyar ta iya gano wata tawada da take a fuskar Salman wacce ta nema ta rasa a fuskar Annur. Ta jima tun suna yara tana masa zancen tawadar, har wata rana yake ce mata da yana da yadda zai yi ya cire ya ba ta ita da ya yi, sai dai kuma babu hali. Ba kowa ba ne zai iya kula da ita, saboda ta kusa da wuyansa take, ita ma saboda tun suna yara ne ya sa ta iya fahimta. Yanzu kuwa ta darara idonta sosai babu ita. Sannan kuma kamar fuskar wannan ɗin ta fi walwala fiye da ta Salman. Duk da ba wai dariya ya yi ba, amma daga yanayin yadda yake za a iya sanin cewa mutum ne shi mai faraa fiye da Salman. "Na tabbata a shirun nan da kika yi kin gano bambancinsu, ko da kuwa kaɗan ne." Kai ta ɗaga mata cike da mamaki. Kafin ta buɗi baki ta ma Maryama tambaya ita ta riga ta yin magana. "Kenan dai ƴan biyu ne..." "Amma kuma ai aunty ta ce mana gudan ya rasu." "Duk ma dai yadda za a yi ƴan biyu ne Yamairah. Salman ɗin ku shi ne Sans. Ko?" "Ehh. Aunty ta saka masa wannan sunan, saboda ɗan fari ne. Please yana ina yanzu?" "Yana gidan su wannan..." Ta gwada mata Annur da hannu. "Gidan su yayan Uncle Marwan." Ta ƙwalalo ido. Kai Alhaji Marwan ya jinjina mata. "Ku faɗaɗa min maganar." Ajiyar zuciya Maryama ta sauke. Ta labarta mata kaf abin da ta sani, tun daga farko har ƙarshe. Ta ɗora hannunta a ka, "Yaushe Yaya Salman ya zama riƙaƙƙen mashayi? Yaushe ya zama mazinaci ban sani ba? Ba halinsa ba ne, wallahi ƙaddara ce ta miyar da shi haka. Yaya Salman ɗina mutum ne mai tsoron Allah. Mutum ne mai ilimin addini, da sanin hukunce-hukuncensa." Ta kuma sakin wani kukan. "Ni yanzu mamakin da nake yi, ta yaya Annur ya dawo hannun su Yaya IA? Ina nasu ɗan da suka haifa yake?" "Ni kaina ina son sanin hakan. Amma kam alamu sun tabbatar cewa Yah Noor ba ɗan su Momy ba ne. Twin brother ɗin Salman ne, yaya ga Yamairah." "Tirƙashi!" Alhaji Marwan ya ambata a fili. * Ƙarfe biyu da rabi Hanan ta gama haɗa komai ta jera a dining. Ta nufi ɗaki ta samu Janan ta yi wankanta ta cancaɗa kwalliya, ta saka doguwar rigar roba amma ba mai bin jiki ba. Ta tasa waya a gabanta tana ta famar yin selfie. Hanan ta gyaɗa kai. "Sannu da aiki Hajiya Janan." Ta kanne ido haɗe da karkace baki ta ɗauki wani hoton, sannan ta ce, "Yauwa ke dai ƴar albarka..." Ta sake karkace baki ta ɗauki hoton. Hanan ta yi dariya sannan ta nufi toilet ta yi wanka. Tana fitowa ta kimtsa cikin riga da skirt na atamfa da Momy ta siya mata. Saboda ita kam tana son native dresses, duk da cewa ba a ƙasar Hausa suka tashi ba. Ta feshe jikinta da turare sannan ta fice daga ɗakin. Fira suka yi da Mony sama-sama har aka fara kiran la'asar Momy ta je ta gabatar da tata. Tana dawowa suka jin horn alamar su Dady sun iso. Aikuwa ihu Hanan ta yi haɗe da ficewa a guje domin tararsu. Janan ma daga ɗakin ta fito tana yin video ta snap chart har ta kusa kai ma Momy karo sanann ta farga. "Idan ba ki ajje wayar nan ba sai na faffalla miki mari." "Tuba nake ranki ya daɗe." Ta ɗora wayar bisa hannun kujera sannan ta bi bayan momy suka fice waje. Sosai suka yi farin-ciki ganin yadda Sans ya warware kamar bai taɓa jin ciwo ba. Kwana ashirin ba wasa ba. Suka rankaya zuwa falo. Ya jiki suka hau yi masa yana amsa musu da walwala. Kafin suka rankaya zuwa dining table ɗinsu mai kujeru shida, suka jera. Hanan ce ta yi serving ɗinsu, cike da farin-ciki da jin daɗi suke cin abincin, Janan na ta famar surkullenta da ta saba. Sai da duk suka ƙoshi sannan suka watse. Momy ta buƙaci ganawa da Sans domin ta masa nasiha. Bedroom ɗinta suka nufa. Nan ta hau yi masa faɗa cikin ruwan sanyi take tafasa shi. Ta masa nasihu masu ratsa zukata, sannan a ƙarshe ta masa addua, haɗe da ba shi izinin tashi ya tafi zuwa ɗakinsa. Wanka ya watsa sannan ya ɗauro alwalla. Bayan ya gama sallah bai sauka daga bisa kafet ba sai da ya yi istighfari sosai, yana mai tsananin nadama. Sai dai fa damuwar nan ɗaya tana nan addabe da zuciyarsa. Tararrabin ranar da asirinsa zai tonu yake. *** *To mutanena...an zo wurin fa. Wasu sun ce wai bakin Amrah ya gwanance da faɗin an zo wurin😀 to ba bakinta ba ne. Alƙalamin ne ya saba da faɗar an zo wurin, kuma saboda an zo ɗin ne ya sa yake rubutawa...lol🤣* *Me za ku ce game da wannan shafin?* *Na warware muku sirrin auren Yamaira da Alhaji Marwan? Kun ga ta yadda rayuwarta ta dawo Katsina? Kun ga yadda ta kuɓuta daga hannun ƴan ta'adda?* *Idan har kun gani da gaske kuma kun gode, I need more comments here.* *Ita kuma ƙawata Janan da ta ɗauki diary, ta kuma rantse sai ta karanta, ko ya abun zai kaya?* *Da gaske ina son Janan, ina ma dai za ta yi ƙawance da ni🤣😀* *Tafiyar tamu tana ta gangara. Sannu a hankali alƙalamin ya kusa sauka. Insha Allahu.* *Masu mutunci sannunku da aiki, sannunku da jimirin kankaro shi. Aikinku na kyau. Keep it up durlings.* Thanks all. Pinky durling💞 RAZ 2 [9/24, 11:51 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taɓa zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 7⃣0⃣ Wattpad: PrincessAmrah *** Sai da ta sha ruwa sannan Alhaji Marwan ya ce da ita ta tashi su tafi, cewa gobe za su sake dawowa su ɗauki Maryama da Annur ɗin, sai su gana da Dr. Hamdan a gidansa. Har gaban motarsu Maryama ta raka su, sannan ta dawo dafe da kanta, har yanzu al'ajabi bai kau daga zuciyarta ba. Tunanin yadda rayuwar Annur ta dawo a gidan su Momy kawai take, da kuma yadda aka yi aka ce wai Annur ɗin ya mutu a lokacin da aka haife sa. Ajiyar zuciya ta sauke, sannan ta ce da Annur ya tashi su nufi sallah, saboda tuni aka kira magrib ɗin. Tashi ya yi suka tafi jiki babu ƙwari, shi kanshi kallo guda za ka masa ka tabbatar cewa ba ya cikin walwalarsa. * A hankali ta leƙa fuskar Hanan, ta tabbatar da ta yi barci sannan ta ɗaga pillow ɗinta ta jawo diary ɗin Sans. Buɗewa ta fara yi, anan ta ga head line na Bama da kuma exact day na ranar da ƴan ta'adda suka fara kawo musu hari. Tun daga harbin da ya ji an ma Abbunsu, izuwa fitarsu daga gida, suka zauna a kango, har tafiyarshi zuwa siyar da wayarsa bai bari ba. Duk abin da ya faru a wannan ranar har komawarsa Maiduguri da motarsu da ta lalace a hanya, dawowarsu bayan ya siyo musu, harbin ƙafarsa da aka yi abinci duk ya rubuta. Ta dafe kanta cikin mamaki. Tunani ta fara yi kodai ba na Uncle Noor ɗinsu ba ne? Sai dai kuma hotonsa da ta gani a next page ya tabbatar mata da cewa nasa ne. Amma kuma a ina ya samu suna Salman (Sans)? Tambayar da ta gaggauta yi wa kanta kenan. Ba ta kai ga samun amsarta ba ta buɗo shafin gaba. Nan kuma duk abin da ya faru washe gari ne a rubuce. Mutanen da suka zo suka tsotse man motarsa suka tafi da shi Maiduguri, kai shi asibiti da suka yi, zaman da ya yi a can har ranar da aka sallame shi. A wannan gaɓar hawaye sosai Janan ke yi, mamaki bai gushe daga saman fuskarta ba. Ta sake buɗo wani shafin, sai ta ga hoton Sans ɗin wanda yake a cikin yanayi na damuwa. Daga ƙasa an rubuta "Tun daga lokacin da na zama gurgu na tsani kaina, na tsani komai nawa. Kamar yadda fuskata babu annuri a wannan hoton, to haka na kasance tun sadda aka naƙasa min ƙafa." Ta matse ƙwallarta, haɗe da buɗo next page. A nan kuma tafiyarsa ce daga Maiduguri har zuwa Katsina. Ƙalubalen da ya fuskanta a tafiyar, da kuma bawan Allah'n da ya haɗu da shi a mota wanda har ya saya masa abinci. Isowarsa tasha da fizge masa kuɗin da aka yi sadda yake kan keken guragunsa. A shafin gaba kuma haɗuwarsa da Farouk Sardauna ne. Silar haɗuwar tasu da kuma taimaka masa da ya yi ya kai shi gidan gonarsu. Ta sake buɗo wani shafin, sai ta ga hoton Bobby wanda ya saki kyakkyawan murmushi a ciki, daga ƙasa an rubuta, "He always smiles. He helped me, and never forget him in my mind. Ina fatar ranar da Allah zai kawo min hanyar da zan rama taimakon da ya yi min, ko da kwatankwacin wanda ya min ɗin ne." Ta buɗo wani shafin. Date da time ne duka a rubuce na ranar da ya fara shan kayan maye. Ya rubuta, "Ba na so, amma damuwa da ta yi min yawa ta sa na fara. Na kuma ji daɗin hakan, saboda ban ƙara shiga cikin damuwar rashin dangina ba tun daga sadda na zama drug abuser." Shessheƴar kukanta ce ta tada Hanan. Cikin magagin barci ta yi firgigit ta buɗe idanuwanta. "Janan whats wrong with you? Why are you crying?" Ta yi saurin ɓoye diary ɗin, ta share ƙwallarta. "Its nothing." Ta ƙirƙiro murmushi. Zaune ta miƙe Hanan. Ta ce, "There must be something wrong, Janan. Ke ɗin nan da ba kya kuka, amma look at your face, tears sun gama wanke cheeks ɗin ki. Janan kina da wacce ta fi ni ne?" Ta gyaɗa kanta. "To me ya sa za ki ɓoye min damuwarki? Mene ne kike ɓoyo da wancan hannun?" Ƙarfafa kukan nata ta yi Janan, ta ce, "Hanan akwai damuwa fa, damuwa mai girma. Uncle Noor..." Ta kwashe duk abin da ta karanta ta sanar da ita, tare suka ci gaba da jimamin cikin kuka, sannan suka ci gaba da karantawa. Abin da ke gaba rubuce shi ne haɗuwarsu da Annur mahaukaci a daji, da kuma ɗaukarsa suka miyar zuwa gidan gonarsu. Tafiyarsa ya haɗu da foster da ake cigiyarsa, sauya kayan Annur zuwa jikinsa, aske gashin kansa zuwa irin na kan Annur, yadda aka yi ya dawo gidan lokacin da Bobby ya kawo shi. Duk babu abin da ya ɓoye a diary ɗin. Kallon junansu suka yi, sun kasa tsayar da hawayensu. Mamaki bai gushe daga zuƙata da fuskokinsu ba. Hanan ta yi sauri ta buɗo shafin gaba. Aikin da boka ya musu ne a farkon shafin, yadda aka jiyar da hankalin kowa, aka kasa ganin ko ɗison bambancinsa da Annur, da canjin aikinsa a kamfanin Dady daga mai zane zuwa ga CEO, rabuwa da abokan ainahin Annur, shaƙuwarsa da Bobby kaf sai da ya zana. "Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!" Hanan ta faɗa hannunta a ka. "Why did you do this? Me ya sa za ka yaudari su Dady? A ina ka kai mana Uncle Noor ɗinmu?" Kalaman da ke fitowa daga bakin Janan kenan cikin kuka. Suka sake buɗe wani shafin. Haɗuwarsa da Maryama ne a jiki, ranar da daga kallo ɗaya ya fara ƙaunarta, faɗan da Dady ya masa a kan fara rugujewar company saboda sakacinsa, zuwansa wurin boka ya masa faɗa a kan true love, aikin da aka masa aka cire masa ƙaunar Maryama, duka ya rubuta. Shafin gaba kuma damuwar da ya fara shiga lokacin da Farouk Sardauna ya fara ciwo ne. Farkon zuwansu likita da kuma gargaɗin da aka musu game da smoking. Tsanantar ciwon Bobby, da kuma damuwar da suka shiga sosai na ciwon nashi. Next page hotonshi ne ya dafe goshinsa yana kuka sosai, a ƙasa ya rubuta "Unforgetable day, the night that my best ever friend gone, and gone forever" Da date da komai na ranar, ya kuma rubuta irin raɗaɗin da zuciyarsa ta shiga. Suka sake buɗe wani shafin, alƙawarin da ya ɗauka na daina smoking da duk wani mugun hali ne a ciki. Suka kalli juna cikin kuka sosai, duk da sun ji haushinsa daga farko, amma a nan sai suka fara tausaya masa. Bai kyauta ba abin da ya yi, amma idan aka yi la'akari da jalalar rayuwa da ya gani a baya, dole a ji tausayinsa. Suka sake buɗe wani. Alƙawarin Bobby da ya so cikawa ne a jiki, sai dai hakan bai samu ba, ya haƙura da Maryama har abada. Shafi na biyun ƙarshe suka buɗe, hoton shi ya duƙar da kansa ƙasa, ya rubuta, "Hukuncin ƙarshe da zuciyata ta yanke min." Suka buɗo shafin ƙarshe, wanda ya rubuta, "I've decided to kill myself. Na so na taushi zuciyata, amma abun ya gagara. A lokacin da nake yin wannan rubutun, kuka nake sosai, na yi shi ne musamman domin duk wanda ya yi farko a karatun diary ɗin nan ya tabbatar cewa ba haka kawai Salman ya so kashe kansa ba. Rayuwar ce ta juye masa baki ɗaya. Farin-ciki ya ƙaurace masa. Ina roƙon duk wanda ya fara karanta diary ɗin nan, ya samu Dady da Momy cikin nutsuwa, kar ya tayar musu da hankali, sannan ya ba su su karanta. Idan kuma a cikin Dady ko Momy ne suka fara karantawar, ina mai roƙon gafararku, ku gafarta min na basajar da na muku, na zauna da ku a matsayin ɗanku da kuka haifa. Na gode ƙwarai da tarayyata da ku, ku ɗin mutanen kirki ne, wanda samun kamarsu a daidai wannan lokacin zai yi matuƙar wahala. Ɗan ku Annur yana raye, sai dai an masa kurciya, da ko ni kaina ban san inda yake ba yanzu haka. Please forgive me, once again." Ya saka full stop a daidai nan. Rungumar junansu suka yi su duka biyun, kuka sosai suke yi, suna matuƙar jin daɗi da Allah ya sa Sans ɗin bai mutu ba. Duk da abin da ya aikata, suna son shi a hakan, matsayi da darajarsa kuma suna nan a cikin zuƙatansu. Rufe diary ɗin Janan ta yi, babba ne kamar girman photo album, sannan ta ajje a gefenta. "Duk da kuskuren da ka tafka ka ba ni tausayi." Hanan ta faɗa. Janan ta ce, "Mu bari har da safe sannan mu kai ma su Momy su karanta ko?" Hanan ta ce, "Janan tunda dai bai mutu ba mu yi haƙuri mu binne maganar nan, ba mu san kalar hukuncin da su Dady za su ɗaukar masa ba. Kin ga ya ce idan aka kore shi daga nan bai san inda rayuwarsa za ta faɗa ba. "Dole za a faɗa musu, Hanan. Idan har muka yi shiru to Allah zai iya kama mu da laifin yaudara. Na san halin Dady, kamar yadda na san halin Momy. Na tabbatar cewa ba za su ƙi shi ba. Za su masa uzuri, sannan kuma za su tashi tsaye neman Uncle Noor." Hanan ta yi shiru, kafin ta ce, "You are right Janan. But ni dai I can't tell them. Wallahi ba zan iya sanar da su ba, don ban san halin za su shiga ba bayan sun ji." "Ni zan sanar musu, yanzu ma ba sai gari ya waye ba." Hanan ta riƙo ta, "Janan me kike shirin aikatawa a cikin daren nan? So kike yi ki hana su barci?" "Hanan please let me tell them. Da safe kuma idan ya shigo ta yaya zan iya faɗa musu a gabanshi?" Shiru Hanan ta yi kawai ta koma ta kwanta. Damuwa lulluɓe da zuciyarta, zullumi da fargaba take tsananin ji. Ta sauka daga bisa gadon, haɗe da nufar ɗakin Dady. Knocking ta yi a hankali ta ji shiru, hakan ya sa ta ƙara yi. "Waye?" Ta ji muryar Dadyn ya faɗa. "Janan ce Dady." "Lafiya?" Ya ce bayan ya buɗe mata ƙofar ido a buɗe. Diary ɗin hannunta ya kalla. "Me ya faru?" "Dady akwai matsala." Ta share hawayen da ya kuma sauko mata. Ya kunna wutar ɗakin sannan ya kama hannunta zuwa bakin gado. Motsinsu ya sa Momy ta buɗe idanuwanta, tana ganinsu ta gaggauta murtsukar idanuwan haɗe da tashi zaune tana tambayarsu abin da yake faruwa. "Ni ma kaina ban sani ba Suhaila. Shigowarta kenan ɗakin tana kuka." "Subhanallahi! Janan ba ki da lafiya ne?" Ta gyaɗa kanta. "Whats your problem? Where is Hanan?" "Tana ɗaki." Ta miƙo ma Dady diary ɗin. "Dady I want you to please read this. Amma don Allah ba na so ku tashi hankalinku. Shi al'amarin Allah duk inda kake ba ka tsallake shi. Ku ɗauka a zukatanku cewa wannan ƙaddararku ce, kuma dole sai ta faru da ku." Cikin mamaki da kiɗima Momy ta ce, "What are you saying, Janan? Me ke a cikin littafin?" "Ku karanta Momy. And calm down, idan ba ki nutsu wurin karatun ba ba lallai ki fahimci wabi abu ba." Ta miƙe da kuka ta bar ɗakin haɗe da jawo ƙofar ta rufe. * WASHE GARI Da sassafe ta tashi kamar kullum, ta nufi kitchen. Dankali ta fere ta yanka sannan ta tsane a kwando ta barbaɗa gishiri. Ta ɗora mai a kasko bayan ya yi zafi ta zuba dankalin. Tarugu da albasa ta yi grating sannan ta yayyanka hanta ƙanana-ƙanana. Ta zuba hantar a pan da ruwa kaɗan, ta saka kayan ƙamshi da albasa da maggi. Bayan ta dahu da zuba mai kaɗan a ciki ta soya sama-sama, ta juye tarugun a ciki ta hau suya. Ba wani soyuwa sosai ta yi ba ta zuba maggi da curry, sannan ta fasa ƙwai guda ɗaya a ciki ta hau juyawa. Bayan ta soyu ta juye a ƙaramin bowl, sannan ta kwashe dankalin saboda wuta kaɗan ta saka dana don kar ya soyu da wuri har sai ta gama sauce ɗin. Plate mai ɗan faɗi ta juye dankalin a ciki, ta nemi foil paper ta lulluɓe shi da bowl na sauce ɗin sannan ta kwasa ta kai dining. Electric water flask ta jawo daga jikin socket ta ɗora a table ɗin. Ta buɗe dining carbinate ta haɗo komai sannan ta nufi ɗaki. Ta samu Annur har ya gama shiryawa cikin ƙananan kayan da ta ajje masa. Sai famar zuba ƙamshi ɗakin yake yi, ya yi zaune ya ƙura wa wuri ɗaya ido. Magana ta masa har sau biyu bai ji ba. Ta tafa hannu a daidai fuskarsa ya zabura. "Mi amor." Ta ɗan cunno bakinta bayan ta zauna kusa da shi. "Ka sha kyau sosai." Ya yi murmushi. "Tunanin me kake?" Dariya kawai ya sakar mata, ya yaƙe duka bakin nasa. "Anyways, lets go and have a break fast." Ta ɗora tafukan hannayenta, shi ma ya ɗora nashi a kan nata. Tare suka nufi dining area ɗin. Dama ta yi wankanta, ta saka ƙananan kaya riga da wando amma rigar mai ɗan tsayi ta kai guiwa. Bayan sun zauna ta hau ba shi a baki, sannan ita ma ta ba kanta. Da haka har suka ƙoshi. Saƙale da hannu suka dawo falo. Ta kunna kallo sannan ta nufi bedroom ta ɗauko wayarta. Tana dubawa ta ga missed call na Dr. Hamdan Ramat. Ta iso falon daidai sadda take latsa kiransa tana Allah-Allah ya ɗauka. Bugu biyu kuwa ya ɗauka da sallama. Amsa sallamar ta yi sannan ta gaishe shi. "Maryam na kira ne in faɗa miki na taho ina hanya ma. Amma ban san yadda za mu haɗu ɗin ba. Tambayoyi ne kawai zan ma mara lafiyar kafin in gano haƙiƙanin damuwarsa ta nan ɗin. Daga nan sai a ba shi duk maganin da suka dace da shi." "Ok Dr. Dama na fara tunanin ko za mu je gidan kawunsa ne, sai mu yi maganar a can." "To babu damuwa. Sai ku yi saurin shiryawa saboda few KM suka rage min zuwa Katsina. Ga shi kuma ba kwana nake son na yi ba." "To bari ma mu tafi yanzu, sai mu jira a can ɗin. Allah ya kawo ka lafiya. Na gode." Har da ɗan rusunawa ta yi tamkar tana a gabansa ne. Tana gamawa ta latso kiran Kawu Marwan. Bai ɗauka ba sai ya katse sannan ya sake kiranta ta ɗauka. "Uncle dama Dr. Hamdan ne ya kira ni yanzu, cewa ya yana daf da ƙarisowa cikin Katsina. Wai yau ɗin nan yake son barin garin." "To ku jira yanzu in zo in ɗauko ku." "Mun gode uncle." Girmamawar da Maryama gare ta kaɗai ya isa ya siye mutanen da suke zagaye da ita. "Yah Noor yanzu kawu zai zo ya ɗauke mu. Don Allah duk tambayar da likitan ya maka ka ba shi duk amsar da ka sani. Kar ka je ka yita yaƙe bakin nan haka nan, ba wani abu zai fahimta ta haka ba." Ya ɗaga mata kai. Tashi ta yi ta nufi ɗakinta. After dress ta zaro daga cikin kayanta ta saka, sannan ta yi veiling da pink kashka. Koda ta fito wayarta na ringing. Uncle Marwan ta gani, da sauri ta ɗauka, ta ji yana ce mata su fito yana ƙofar gida. Hand bag ɗinta ta saɓa sannan ta ce da Annur ya tashi su tafi. Ta datse ƙofar falon ta jefa mukullin a jakarta. Sadda suka je bakin gate ta shaida wa mai gadi cewa za su fita sai zuwa anjima za su dawo. Ya musu addua da fatar alkhairi sannan suka fice. Bai ko kashe motar ba suka same shi, ta buɗe wa Annur gaban motar ya shiga sannan ta rufe, ita kuma ta zauna a baya. Suna isa gidan mai gadi ya wangale musu gate suka ƙarisa ciki. Ita ta buɗe ma Annur motar ya fito, sannan ta kama hannunsa suka bi bayan Uncle Marwan ɗin. Cikin gidan ya nufa da su. Ya samu falon babu kowa, ya basu umurnin zama su jira shi a falon. Bayan ya hau sama ya samu Yamaira a kwance fuskar nan tata ta gama kumbura da kuka. Ya ce, "Wai ni kam Yamaira wannan kukan ba zai tsaidu ba haka nan? Ina amfanin abu guda tun jiya? Ni a tunanina za ki ɗaga hannu sama ki gode wa mahaliccinki da ya bayyana miki ƴan uwanki har biyu, ba tare da zato ko tsammaninki ba? Ki cire damuwar, don Allah. Ki sauko ƙasa ga su Maryama nan sun iso ita da Annur. Likitan wai yana bisa hanya." Ta lallaɓa ta tashi zaune. "Bari in samu watsa ruwa in sauko." "Yauwa dai, please wipe the tears and let them go. Ki hanzarta shiryawa, na bar su falo su kaɗai." Ya ɗauko Yesmeen suka sauka zuwa falo. Kallo ya kunna musu, tashar NTA suna kallon news. Yamaira ba ta wani jima ba ta fito cikin naɗin lafaya baƙa mai manyan zanen light blue. Duk da kukan da ta sha, amma hakan bai hana ta yin kyau ba. Bayan sun gaisa ta koma kan kujera kusa da Maryama ta zauna. Ta ce, "Ashe ma dai da wuri haka likitan zai zo." "Wallahi kuwa. Ni ma kaina ban sani ba, a tunanina isowar yamma zai yi, kwatsam na ga kiransa cewa ya kusa ƙarisowa Katsina, kuma sai ya fara ganin Yah Noor sannan." "Allah sarki!" Ta kalli Annur. Wata irin nutsuwa take jin tana saukar dukkan gaɓar jikinta. Sosai take jin daɗi, take kuma ganin abun kamar a mafarki. A tunaninta ta rasa kowa nata, sai dai Allah da naShi lamarin, ashe har ma da ƙarin wanda ba ta sani ba. Iyayen nata dai ne ta rasa, rashi na har abada. Sai ta ji hawaye na saukar mata, ta gaggauta share su don kar mai gidanta ya gan ta tana kukan. Ƙarar kira Maryama ta ji a wayarta, ta duba ta ga Dr. Hamdan ne, ta gaggauta ɗauka da karawa a kunnenta. "Ga ni na shigo cikin Katsina. Ga shi kuma ban san komai ba, so ɗaya na taɓa zuwa Katsinar ma tunda nake, kuma shekaru ba adadi." "Ok Dr. To ko za ka samu mai kabu-kabu ne sai na masa bayani?" "Tunanin da na yi kenan. Ina zuwa." Ya tsinke kiran. Ba a daɗe ba ya sake kiranta. Suka yi magana da mai mashin ɗin, ta masa bayanin gidan, ya ce mata ya gane. Minti ashirin da biyar ya isar da su gidan Alhaji Marwan. Ya sallami mai mashin ɗin sannan mai gadi ya buɗe masa gate kamar yadda Uncle Marwan ya umurce shi. Mai gadin ya masa iso har cikin gida, suka shiga cikin falon tare. Dr. Hamdan M. Ramat mutum ne mai tsananin ƙwarjini da kamala. Fari ne mai faraa, ya ɗan dattijanta sai dai ba sosai ba. Ya shigo ya zauna fuskar nan tasa kamar koyaushe da walwala. Har ƙasa suka duƙa suka gaishe sa. Uncle Marwan kuma ya ba shi hannu da sakin fuska suka gaisa. Kallo ɗaya ya ma Annur ya ce, "Wannan ne mara lafiyar?" Maryama ta amsa masa da ehh. "Amma dai ya samu sauƙi ko? Ji idanuwansa fa. Kallar ni nan ka ji?" Ya ɗora dukkanin idanuwansa ga Annur ɗin da shi ma shi yake kallo, sai dai yana ɗan kauce idonsa. *** *Wash Allah! Na gaji. Iya wannan ya samu. Fatar dai kun ji daɗinsa. Kun ga dai yadda tafiyar ke ta gangara.* *Wannan shafin sadaukarwa ne ga Teemah Sahabie. Sosai na ji daɗin kiran da kika min a waya jiya, musamman don ki nunar min da farin-cikin da kika ji na last page. na gode ƙwarai, Allahu ya bar zumunci.* Thanks all. Pinky durling💞 RAZ 2 [9/26, 12:03 AM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taɓa zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 7⃣1⃣ Wattpad: PrincessAmrah *** This page is in your honour, Ummukulthum Sani. You are indeed a nice soul. I really love and cherish you. Kina cikin best 10 people da suka fi kowa ƙaunar book ɗin nan. Allahu ya bar zumunci da zaman tare. Ina ƙaunarki fisabilillah. *** Hannunsa ya sa ya tallabo fuskar Annur yana kallonsa. "Annur ko?" Dr. Hamdan ɗin ya faɗa. Maryama ta ba shi amsa. Ya saki kan Annur ɗin da ya tallaba sannan ya saki murmushi. "Akwai hasashe ɗaya da likitocin ƙwalwa ke fara yi idan za su duba mara hankali. Suna farawa da kallon cikin ƙwayar idonsa, saboda idan ka kalli idon mahaukaci sosai akwai wata ƴar birkicewa da za ka ga ya yi. To abin da ya ɗaure min kai, idanuwan wannan ɗin normal suke gaskiya. Ku dube shi da kyau." Ya dakata daga nan. "Annur me ya sa kake noƙewa idan na haɗa ido da kai? Kodai ba ka so in gane cewa kana a cikin hankalinka ne?" Dukkansu da ke ɗakin suka zabura. Shiru Annur ɗin ya yi, sai dai kallo guda za ka masa ka hasasho tashin hankalin da yake a cikinsa. "Idan ma dai ka yi haukan a baya, to lallai ka samu sauƙi sosai a yanzu kam. Annur tun yaushe ka warke?" Nan ma dai shiru Annur ɗin ya ƙara yi. "Ban ga amfanin pretending ɗin ba. Dukkanmu nan da muke tare babu bare, ni ne kawai baren amma kuma makusancinka, tunda na duba ka a matsayin likitanka." Ya fasa kuka da ƙarfi Annur ɗin. Ya ɗora dukkanin hannuwansa a bisa kai, kafin a hankali ya sunkuyar da kansa yana kuka mai cike da zallar tashin hankali, da kuma shessheƙar kuka. Su duka mamaki bai kau daga fuskokinsu ba. Maryama a ranta take jinjina kalamin likitan, ta yadda kai tsaye ya zartar da hukunci kan cewa Annur ɗin ya samu lafiya. Amma idan ya samu lafiyar me zai sa ya rinƙa acting kamar bai warke ba? Da sauri ta matsa gare shi, ta tallabo shi cikin hawaye tana rarrasarsa, hankali da ƙwaƙwalwarta sam ba su aminta cewa Annur ɗin ya warke ba. Hasashe ne dai kawai irin na likitoci, tunda dai ba ilimin gaibu gare shi ba. A hankali ya zame daga riƙon da Maryama ta masa, sai gashi ya silalo ƙasa, tafukan hannayensa ya rufe fuskarsa da su, yana kuka bil-haƙƙi. Bubbuga masa kafaɗa Dr. Hamdan ya hau yi. "Ba kuka na sa ka yi ba Annur. I just want you to tell me, why are you pretending? Akwai damuwa ne?" Sai a nan Uncle Marwan ya ce, "Annur talk mana. Ka yi shiru ka daina kukan da kake yi kuma." Sai a sannan ya ce, "Haƙiƙa na ji sauƙi, tun daga ranar da na fara ganin zoben hannun Maryama..." Cike da mamaki ta ɗago kai tana kallon shi. Mafarki take yi kawai ta riya a ranta. Saboda ba ta taɓa tsammani ba. Wai ma me yake faɗa ne? Murmushi Dr. Hamdan ya saki. "Wasu mutanen sai su rinƙa ce ma likitocin ƙwalwa wai tamkar masu aiki da jinnu, ko kuma suna da ɓoyayyen tsafi. Alhali kuma ba haka ba ne. Karatu ne kawai mutum ya yi mai zurfi, fannin ƙwalwa kai tsaye da kuma psychology, wanda hasashenmu ke hasko mana wani abu, cikin salo da dabara muke gano gaskiyarsa. A sadda na duba Annur, ban tabbatar cewa yana a cikin hankalin nasa ba. Sai dai tun sadda na shigo, kallo ɗaya na masa na hasko cewa da hankalinsa. Saboda yanayin zamansa, dariyar yaƙe da yake saki sam! Ba irin na mahaukata ba ne. A nan duk ban gasgata ba, sai sadda na umurce shi da mu haɗa idanuwa ya noƙe, sai na ƙarisa gasgatawa. Saboda duk wanda za ka buƙaci ka haɗa ido da shi ya noƙe, lallai akwai wani ɓoyayyen al'amari a tattare da shi. Ko ga mace ma, ka nemi haɗa ido da ita ta noƙe, to cikim biyu akwai ɗaya. Kodai ba ta da gaskiya, ko kuma ta yi zurfi a ƙaunarka. To me zai sa daga haɗuwa yau ɗaya tal Annur ya noƙe ma haɗa ido da ni? Bayan nan kuma, idanuwansa normal suke, ko kaɗan babu alamun birkicewa a tattare da su. Sai ga shi hasashen nawa ya zama gaskiya. May I go?" Ya miƙe tsaye. Alhaji Marwan ma ya miƙe fuskarsa cike da mamaki. "Dr. Ya za a yi ka tafi daga zuwanka?" "I've done with my job, Mr." Ya saki murmushi. "But Dr..." Ya katse sa. "Duk abin da ya yi saura iyakacinsa tsakaninku. Ba zan so jin sirrin family ba. Ku tattauna komai, ku ji dalilinsa na yin pretending ɗin. Ni zan tafi." Ba don Uncle Marwan ya so ba ya gyaɗa kansa. "To Dr. Ba dai za mu iya biyanka ba. Sai dai mu kamanta..." Ya ɗaga masa hannu fuskarsa da murmushi. "Me na muku da zan karɓi wani abu daga gare ku? Don't worry Mr. Dr. Hamdan is a very simple man. Let me go, please." Hannu ya miƙa masa suka sake gaisawa, sannan ya taka masa har gaban motarsa, yana daɗa yi masa godiya. Ita kam Maryama ba ma ta samu damar yi masa godiyar ba. Mamaki haɗe da al'ajabi ne lulluɓe da zuciyarta. Ta kasa ko da kallon sa ma. Yamaira da ke zaune ma mamaki ne ya hana ta tankawa. Sai famar rirrigar Yesmeen da ke barci take yi. Bayan Alhaji Marwan ya shigo ya zauna kusa da Annur a ƙasa. Ya tallabo shi ya ɗora fuskarsa bisa cinyarsa. Yana ɗan bubbuga bayansa a hankali. "Ka yi shiru ka ji." "Uncle..." Ya faɗa cikin muryar kuka. Sai Alhaji Marwan ya ƙarisa tabbatar da zancen likitan. Yadda Annur ya kira sunansa sosai ya tuno da rayuwar Annur ɗin ta baya, tun yarintarsa har zuwa girmansa. Ya lallaɓa ya tashi zaune. "Uncle haƙiƙa na tsinci kaina a cikin matsanancin tashin hankali, tun daga ranar da Maryama ta fara shigowa inda nake na yi tozali da zoben hannunta. Sai dai tun daga nan ciwon yakan kaɗo min, wani lokaci sai in rinƙa ji na tamkar ba ni ba, sai na tuno da wasu abubuwan, sai kuma in neme su a ƙwaƙwalwata in rasa. Na ci gaba da rayuwa a matsayin mahaukaci ne saboda in gasgata halin da nake ciki ɗin. Na farga na gan ni a gidan wasu wanda ban taɓa sanin da su ba a duniya. Ban san dalilinsu na kawo ni inda suke ba, sai dai na rinƙa jin wasu kalamai a bakinta, wanda suka tabbatar min da cewa aure za a ɗaura mana ni da ita. A duk sadda na ji ni daidai, nakan duba ma'ajiyar Maryama, in ɗauko wannan zoben mai matuƙar daraja a gare ni, in kalla. Wani lokacin ina kuka haka nake kallonsa. Sosai nake ankara da Maryama. Na fahimci yadda take ƙaunata da zuciyarta ɗaya. Take da burin kyautata min, take son ganin dariyata. Akwai ranar da zancen Amrah ya shigo cikin hirarmu, wacce har ga Allah daga farko ban san komai ba, kamar yadda na faɗa muku cewa abin yakan kaɗo min ne. Kamar wasa zancen ya yi tsawo, sai ta rinƙa tuno min da Amrah. A take na rinƙa tunanin yarintarmu da Amrah. Ƙaunatayyar da muka yi wa junanmu. Kyautatawa da kuma soyayyarmu ta tsakani da Allah. Soyayyar Amrah ta daɗa komawa sabuwa dal a lokacin, nake jin ina ma dai a ce Amrah za ta dawo gare ni. Ina ma a ce tafiya ce ta yi zuwa wani gari, komai daren daɗewa za ta dawo a gare ni mu ci gaba da rayuwarmu a tare. A nan ɗin Maryama ta rinƙa kawo min kalamai masu zama zuciya, wanda duk iya taurin zuciyar mutum dole sai ta karaya. Ta nuna min zallar soyayyar da take min a baki, wacce na tabbatar da har cikin zuciyarta hakan ne. A take ta ƙoƙarta share min hawaye, ta saka ni murmushin dole, sannan ta nufi kawo mana abincin da za mu ci. A wasu lokutan har gani nake kamar dai Maryama ta gane cewa pretending ne nake yi, ƙyale ni kawai ta yi. Sai dai kuma yadda take tausayina, jikinta ke rawa take hidima da ni, ta min wanka, ta saka ni na yi alwalla, ta saka mu yi sallah tare, abinci ta ba ni shi a baki, sai na tabbatar cewa har yanzu ba ta fahimci lafiyata lau ba. A ranar da hankalina ya fara dawowa, Umman Amrah ta zo har gidanmu, ta tado min labarin asalin zoben Amrah. A nan ne na tabbatar hankalina ya kammala dawowa gangaar jikina. Saboda ban ƙara jin wata alamar gushewar hankali kamar a baya ba. Ita kanta Maryamar idan za ta ajje hankalinta, za ta iya gano cewa tun daga nan ibadata ta gyaru. Ta sha mamakin ganin ina alwalla daidai, sai kawai ta ɗauka cewa koya min da take yi ne ya sa komai ya daidaita. Haka sallah ma, sai ta ɗauka duk koyawarta ce ta yi tasiri, alhali kuwa hankalina ne ya dawo gangar jikina. Hankalina bai gama tashi ba, sai da na wayi gari da tabbacin wai su Dady ba su ne iyayena ba. A lokacin da Maman Yesmeen ke bayani, ji na yi tamkar in fasa kururuwa mai tsananin ƙarfi, in yi ihun da zai jijjiga kaf ilahirin katangar gidan. Sai dai na saita zuciyata, saboda ba na son a gano na samu sauƙi, don sai na gwammacin halin haukan da nake ciki ma, a kan mugun labarin da kunnuwana suka jiye min, wai mutanen da na rayu da su ba su ba ne iyayena. A baya na yi ɓoyon na warke ne don sanin haƙiƙanin dalilin da ya sa ba a miyar da ni gidanmu gaban iyayena ba, saboda ko ba ta fito fili ta faɗa min ba, na tabbata akwai sadda zancen zai kawo zance ta faɗa min. Wannan shi ne gaskiyar abin da ya faru. Haƙiƙa na wamrke, na kuma samu lafiya." Ya ƙarisa maganar da sharar ƙwallarsa. Komai a mafarki take ganinsa. Ta kasa furta komai, kamar yadda ta kasa daina kallonsa. A wani ɓare na zuciyarta murna ce fal, abin da ta daɗe tana jira, Annur ɗinta ya warke, sai ga shi ashe ma a matsayin warkakke take tare da shi. Wani ɓaren na zuciyarta kuwa, tunani take kamar zai bar ta ne. Kamar ba zai taɓa amincewa da ita a matsayin abokiyar rayuwarsa ba. Maganar da ta ji ya yi ce ta tsamo ta daga duniyar tunanin da ta lula. "A rayuwata tunda na tashi na yi wayo na san Amrah, na kamu da soyayyar Amrah, rasuwarta ta girgiza ni, ta shigar da ni wani mawuyancin hali, wanda na gagara tuna komai na rayuwata. Ban taɓa tsammanin akwai wata mace da zan so bayanta ba. Ban taɓa tunanin cewa Maryama za ta yi tasiri a cikin zuciyata ba. Ranar da na fara ganinta a cikin hankalina, ƙarfin hali da jarumta kawai suka hana na kai mata duka. Kalaman soyayya da take faɗa min, jin su nake kamar ana zuba narkakkiyar darma a cikin kunnuwana, tsabar jin haushinsu da nake yi. Ranar da ta shigo tana faɗa min an ɗaura mana aure kuwa, tamkar in rusa kuka haka na rinƙa ji. Sai dai na daure, na kai zuciyata nesa, na ci gaba da rayuwa da ita. Mamaki bai gushe min ba a ranar da Maryama ta fara shiga ban-ɗaki da ni ta yi min wanka, ta rinƙa runtse idanuwanta, amma duk da kunyar ba ta hana ta tsaftace ni ba. Babu abin da kyautatawa ba ta sakawa. Wannan kyautatawar da ta rinƙa yi min, ita ta rinƙa siyan soyayyarta ta ƙarfi da yaji tana kai wa har a cikin zuciyata. Ita ta sa zuciyata kamuwa da ƙaunarta, duk da cewa ƙaunar Amrah na nan ba ta gushe ba. Duk da hakan nakan tuno Amrah. Nakan tuno rayuwarmu ta baya, da kuma alwashin auren junanmu da muka yi. Sai dai ina tausar zuciyata, a duk sadda na tuno da nasihun Amrah a gare ni, wanda na kasa yin amfani da su a lokacin da ta rasu, har hankalina ya gushe. Wallahi da zuciya ɗaya na kamu da ƙaunar Maryama, nake jin ta har cikin zyciyata. Samun mace irin Maryama abu ne mai matuƙar wahala, wasu halayen nata har suna min kama da na Amrah. Na ƙudurci rayuwa da Maryama har ƴarshen numfashina. Na yi alwashin kyautata mata, kamar yadda ta kyautata min a sadda take tunanin ba na cikin hankalina." Duk da kukan da take yi, hakan bai hana ta sakin murmushi haɗe da ajiyar zuciya ba. Ta rinƙa bin sa da kallo, kallon mamaki. Duk da son da take masa tun da daɗewa, ba ta taɓa tsammanin duk ranar da Annur ya warke zai so ta ba. Sai ga shi wai yau Annur da kanshi, kuma a cikin hankalinsa yake furta mata kalmar so. Ina za ta saka ranta don murna? Alhaji Marwan ya ji daɗi sosai, ya ce, "Ni kaina har ƙarshen rayuwata ba zan taɓa daina jinjinawa yarinyar ba. Haƙiƙa yarinya ce ƴar halak, da ta amsa sunanta ƴar albarka. A cikin halin rashin hankali da kafe, ta turje kan sai ta aure ka. Ta ƙi auren ɗan uwanta da iyayenta suka zaɓa mata, kawai don ta taimaka maka. Sannan kuma ga iyayenta da suka yi risky'n aura wa ƴarsu mahaukaci a matsayin abokin rayuwarta. Ba zan taɓa mantawa da su ba, haka kuma ba zan taɓa daina yi musu addua ba." Annur ya jinjina kansa, yana tuno mutuncin iyayen Maryama da ya karanta a lokaci kaɗan. "Ni yanzu abin da ban sani ba, shi wancan ɗan uwan nawa, me ya sa zai yi rayuwa a gidanmu a matsayin ni ne shi, kamar yadda na ji Maryama ta faɗa wa Yamairah jiya?" Maryama ta ƙoƙarta tattaro magana, ta ce, "Ni ma kaina ban sani ba, abin da na jima ina son sani kenan. Kuma abun haushi, tunda yake a gidan su ba su taɓa ganin wani bambanci a tsakaninsa da kai ba? Na jima ina tunanin nan." Uncle Marwan ya ce, "Allah kaɗai ya bar wa kansa sani, sai ko shi Salman ɗin. Ku haɗa da ni nan kaina, ban taɓa kawo wa raina cewa wai ba ainahin Annur ba ne. Ko kaɗan ban taɓa ganin wata alama da za ta nunar min da cewa Salman ba Annur ba ne. A ganina komai nasu ɗaya ne, basu da bambanci. Sadda su Maryama suka fara kawo min maganar, na sha mamaki sosai, har daga farko na kasa gasgatawa, sai daga baya sannan." Yamairah ta ce, "Suna da bambanci, sai dai kaɗan ne ba mai yawa ba." Annur ya kalle ta. "Kenan dai identical twince ne mu?" Ta ɗaga masa kai. "Wata tawada ce ta bambanta ku, a ƙasan fuskarsa kusa da wuyansa take. Sannan kuma fuskarka ta fi ta shi walwala. A haɗuwata da kai jiya kawai na fahimci haka." "Allah sarki! Allah mai iko! Sarki gagara-misali. Mabuwayi, mai hikima. Allah mai tsara lamurra yadda Yake so. Allah mai aikata abu ta yadda Ya so ya kasance. Mahaliccinmu mai sarrafa abu, ba tare da samun tangarɗa ko kaɗan ba. Idan ba al'amarin Allah ba, ta yaya halittar mutum ɗaya za ta kasance ga mutum biyu?" Uncle Marwan ya ce, "Duk ba abin mamaki ba ne wannan. Fin biyu ma za a iya samun masu kama. Da ake haihuwar ƴan huɗu fa? Ko kwanakin nan wata mata ta haifi ƴan huɗu, kuma duk kamanninsu iri ɗaya ne." "Haka ne Uncle...ahm..." Ya yi shiru alamun yana so ya yi magana. "Say it out ɗana. Akwai damuwa ne?" "Uncle tunda dai haka abun ya kasance, ina da buƙatar komawa gida, sosai nake son ganin Dady da Momy, da kuma ganin ɗan uwana, ya faɗa min dalilinsa na yin pretending a matsayin shi ne ni." *** Kuka take sosai, har muryarta ta disashe tsabar kukan. Duk da cikin halin da yake, shi ɗin ma tashin hankali ya gama garwaye jiki da jinin jikinsa, amma bai hana shi rarrasarta ba. "Ba na so kina kukan nan Suhaila. Ina so ki ƙaddarta tamkar komai bai faru ba har zuwa safe, ko za ki samu ki iya runtsawa." "Alhaji me ya sa zan yi shiru? Me ya sa zan iya runtse idanuwana da nufin yin barci bayan tashin hankalin da nake cikinsa? Ka faɗa min Alhaji, ta yaya zan iya daina kuka bayan na yi zama tare da mutumin da ba ɗana ba, tsawon shekaru da dama a matsayin ɗana?" Ta gyaɗa kanta, hawaye sharkaf da fuskarta, duk ya gama sauka ya wanke wuyanta. "Na sani sarai Suhaila, cewa ba abu ba ne mai sauƙi. Wannan wani gagarumin abu ne, da ba mu taɓa tsammanin faruwarsa ba. Sai dai ina so mu taru mi miƙa al'amarin ga Allah, kar hakan ya sa mu manta da ƙaddararmu, wacce duk dabararmu ba za ta taɓa nisantarmu ba." "Alhaji..." Ta yi shiru. "Ki daure dai Suhaila. Ina gudun kar wannan damuwar ta jawo wata babbar damuwar." "Alhaji gwara ma in mutu a kan wannan baƙin daren da nake a cikinsa yau. Ban taɓa tsammanin akwai ranar da rayuwa za ta birkice mana kamar haka ba. Manya-manyan abubuwa biyu sun faru a baya, amma hankalina bai tsananin tashi kamar na yau ba. Me ya sa yaron nan zai mana haka? Wane dalili zai sa ya raba mu da gudan jininmu, ya dawo a ƙarƙashin inuwarmu da zama? Alhaji ka duba fa ka ga, ashe har da shirka, ya haɗa mu da boka, don kar mu taɓa kawo wa ranmu cewa ba ɗan namu ba ne. Me ya sa rayuwa za ta min haka? Me ya sa?" Ya jawo ta ya ɗora kanta a bisa cinyarsa. Tamkar ƙaramar yarinya haka ya rinƙa rirrigarta. "Duk ba wannan ne abun damuwar ba yanzu, sanin haƙiƙanin inda Annur ɗinmu yake ne abin ji. Sanin halin da yake ciki, da kuma inda yake." Ta tashi zaune. "Alhaji shi ne kuma kake tunanin zan iya yin barci a wannan halin? Ban san halin da ɗana yake cikinsa ba. Ban san a wace rayuwa yake ba yanzu. Ban san duniyar da ya faɗa ba. Ya ce kurciya aka masa. Alhaji ko ka san cewa kurciya har ƙasar ma baki ɗaya mutum yana iya bari? Kila ma an kashe min yaro. Wallahi matuƙar an kashe shi kuwa, tabbas da wannan hannuwan nawa zan kashe Salman. Da wannan hannuwan zan luma masa wuƙar da ya luma wa kansa, sai dai a wannan karon zai mutu ne kai tsaye. Sai ya baƙunci lahira, in ya so ni ma ɗin a kashe ni." Ya yi saurin doɗe mata baki. "Haba Suhailah! Me kike faɗa ne haka? Idan rai ya ɓaci, hankali ba ya gushewa. Ban tsammaci jin kalmar kisa ta fito daga bakinki ba. Ko ma dai miye, idan ma mutuwar ya yi ai sai mu sada shi da hukuma, ita ta san matakin da za ta ɗaukar masa. Amma ɗaukar mataki da hannunmu ai wani babban laifin ne." "Ban damu ba don na yi wani laifi a yanzu. Annur kaɗai na mallaka a matsayin ɗa namiji. Ta ya wani mugu zai zo kwatsam ya raba mu? Karya ne! Wallahi bai isa ba!" Sosai ta dake a daidai wannan lokacin. Hawayen ma ta daina yinsa, sai saƙe-saƙe da mugayen ƙudirirrika a zuciyarta. Da haka har asubah ta yi, Dady ya nufi masallaci, ita kuma Momy ta tashi jiki babu ƙwari ta yi tata. Sosai take jin kanta na sara mata, tsabar kukan da ta sha, ga kuma uwa uba rashin barci. A kan darduma ta zauna har gari ya ƙarisa wayewa, zuciyarta ƙagare da yin arba da Sans. *** *My pipu how was this chapter? So so so...ba zan ƙarisa ba, idan ta muku daɗi to ku da kanku ku ƙarisa in ji.👂* *Hehehe! Mun dai ji ƙudirin na Momy, ko ya abun zai kaya? Ga dai gari ya waye, duk mai faruwa a yau za ta faru, sai mu yi tsumayen shafi na gaba, insha Allahu za mu warware komai.* *Na yi tsammanin daga wannan shafin sai na ƙarshe, to kuma dai abun bai kasance ba, ashe ya fi haka. Ko ma dai nawa ya rage, ku juri bibiyata, na tabbata dai ba za mu ƙara shafi huɗu nan gaba ba ba tare da ya ƙare ba. Da yardar Allah.* *Don't forget to vote,* *Comment,* *And share with your family and friends.* Thanks all. Pinky durling💞 RAZ 2 [9/27, 12:36 AM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taɓa zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 7⃣2⃣ Wattpad: PrincessAmrah *** Momy ta yi zaune falo da kumburarrar fuskarta. Ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya, jiran fitowarsa kawai take yi. A haka Hanan ta fito ta same ta. Ita ɗin ma kanta jikinta babu ƙwari, sai tarin fargaba da tararrabin abin da zai faru a yau take yi. Ta gaishe da Momy cikin girmamawa, sannan ta nufi kitchen domin haɗa kalaci. Rashin kuzarin kirki ya sa ba ta tsiri yin abu mai wahala ba. Kawai sai ta dafa ruwan zafi sannan ta soya ƙwai, tunda dama akwai breadi. Da ta gama ta kwaso komai ta kawo dining. Ɗaki ta koma ta samu Janan ta tashi har ma ta shiga wanka. Kayan sawa ta fito da su sannan ta zauna a bakin gadon har Janan ta fito ɗaure da towel. "Ranki shi daɗe ashe kin samu tashi." Ta ɗaga mata kai. "To ya yi. Ga kaya nan na fitar saura in fito in samu ƙyuya ta hana ki fitar da naki kin saka nawa." Ta yi murmushi. "Ni ba ki ga duk a saɓule nake ba? Damuwa ce linkime a cikin zuciyata. Sosai nake tsoron abin da ka iya faruwa yau." "Insha Allahu babu abin da zai faru sai alkhairi." "To Allah ya tabbatar." Janan ta furta bayan ta zauna bisa stool za ta fara shafar mai. Hanan kuma ta shigewarta wanka. Yana can yana barci shi kuma, sai buɗe idonsa ya yi ya fara hangen haske alamar gari ya waye. Sauƙinsa ɗaya dama ya yi sallar asubah. Sai ya gaggauta tashi haɗe da ɗora idanuwansa ga agogo. Ƙarfe takwas da rabi ya gani, ya tashi tsaye. Toilet ya nufa ya yi brush da wanka sannan ya fito. Baƙin jeans ya saka da farar T-shirt irin ta police wacce ta bi jikinsa, kasantuwarta body hug. Ya feshe jikinsa da turare, ya ɗan ɗaga rigar ya duba cikinsa. An yi ceiling ɗin wurin tamkar wani abu bai faru ba. Sai ka ƙura ido sosai za ka iya ganewa. Nan ya ƙara jinjina wa Indiyawa da wannan baiwar tasu. Shi ya sa da zarar ciwo ya tsananta ga mutum ake tura shi India. Ya ɗauko wayarsa daga jikin chaji sannan ya fito. Haka kawai sai ya samu kansa da faɗuwar gaba. Ya dafe ƙirjinsa haɗe da tsayawa cak! A daidai ƙofar falon. Ta biji-bijin labule ta hango shi, hakan ya sa da azama ta miƙe, sai dai ta ji Dady ya riƙe ta, ya ja ta zuwa bisa doguwar kujera. "Take heart, Suhailah. Wallahi dukkan abin da kika ga ya faru da bawa to dama can haka Allah ya tsara ga rayuwarsa. Jarabawar ubangiji babu ta inda ba ya hukunta ta. Sai dai a ga shin za ka haye wannan jarabawar ko kuwa za ka yaƙe ta? Calm down, don girman Allah. Ki dube ki Suhaila, ko wanka ba ki yi ba tun ɗazu kika fito. A runtse kika kasa runtsawa sai ka ce hakan zai kawo miki mafita. Tunda nake da ke ba ki taɓa jayayya da ni ba. Ban taɓa hana ki abu kika kartake sai kin yi shi ba sai jiya zuwa yau. Why Suhailah?" Sai ta ji zuciyarta ta sanyaya. Amma ji take fa har yanzu ba za ta taɓa iya yafe wa Salman ba. Dole ta ɗauki mataki a kansa, in ya so komai ma zai faru a ƙarshe sai dai ya faru. Ɗaga kansu suka yi su duka biyun a daidai sadda suka ga Sans zaune a gabansu. Ya ji duk abin da suke faɗi, sai dai bai san inda maganar tasu ta dosa ba. Bai ma san cewa da shi suke yi ba. "Momy barkanku da tashi." Ya faɗa cikin sassanyan murmushi. Ƙarfin hali ne kawai ya hana Dady sako masa wani zancen. Ganin irin kallon da suke bin sa da shi kuma duk sai ya tsargu. Ya sake maimaita, "Dady ya gajiyar tafiya?" "Annur..." Tun daga kan sunan da Dady ya faɗa sai Momy ta dakatar da shi da hannu. Cikin masifa take kallon Sans cike da tsana da wulaƙanci. Ta ce, "Point of correction, Alhaji. Annur kodai Salman?" Durum! Sans ya ji gabansa ya yi mummunan faɗuwa. Sai ya saki idanuwansa yana bin Momy da kallo. "Ka kalle ni da kyau, baƙin munafuki. Mugu, macuci, mayaudari, azzalumi, maha'inci malalaci..." Ta shanye kukan da ya zo mata. "To Allah ya toni asirinka mugu! Allah ya fi ka, kuma wallahi sai ka faɗa min inda ɗana Annur yake, ko kuma in yi ƙararka, shari'a ce kawai za ta raba ni da kai." Gabansa ya ji yana bugawa da sauri da sauri. Tamkar ya haɗiyi zuciya ya mutu haka ya ji. Baki ɗaya kunnuwansa biji-biji yake ji tsabar tashin hankali. "Mu za ka yaudara? To Allah ya toni asirinka baƙin makiri." "Don Allah Momy ki saurare ni..." Ya ji saukar mari a kumcinsa. Dafe kumcin nasa ya yi, hawaye na sauka a kansu sosai, zafin marin ya shige sa. "Ka tashi ka bar ɗakin nan, na ba ka daga nan zuwa ƙarfe sha biyu na ranar yau, wallahi idan har ba ka gano min inda ɗana yake ba sai na yi ajalinka, da wannan hannuwan nawa." Ta gwada masa tafukan hannayenta, cike da ba shi tabbacin za ta iya kashe shi ɗin. Jiki babu ƙwari ya miƙe tsaye. Sai yake ƙara yin da na sanin abubuwan da ya aikata a rayuwarsa. Yake jin haushi da bai kasance na-gari ba. Takaicin sauyuwar halayensa na ƙara kururuwa a cikin kunnuwansa. Yana miƙewa jiri ya diɓe shi ya sulale, don dole ya dawo ya zauna. Sosai Dady ya ji ya ba shi tausayi. Ko ba komai labarin da ya bayar a cikin diary ɗin dole za a ji tausayinsa. Jarrabtar da ya gani a rayuwarsa. Halin da ya shiga tun bayan da ƴan ta'adda suka shiga garinsu. Ya runtse idonsa, sai kuma ya rinƙa tunowa da kalaman Sans ɗin a asibiti ranar da yake masa nasiha. To ko ma dai dalilin da ya sa ya roƙi kar ya guje shi duk rintsi duk wuya kenan har abada? Ya share hawayensa. A hankali ya sauko ƙasa kusa da Sans ɗin, ya ɗago masa kansa suka kalli juna, sai dai kunya ba ta bar Sans ya ci gaba da haɗa idon da Dady ba. Da hanzarinsa ya ɗago idonshi, yana kuka mai cike da ban-tausayi. "Salman..." Dady ya kira sunansa. "Haƙiƙa ka tafka babban kuskure, kuskure mai wuyar a yafe maka. Wane irin mawuyancin hali ne za ka shiga wanda zai saka ka yin shirka, ka manta da ubangijinka? Me zai sa ka raba jini da hanta? Haba Salman! Ka cuci kanka, ka kuma ci amanar tarbiyyar da iyayenka suka gina maka. Yanzu abin nan da ka yi, a wace rayuwa kake tunanin Annur ɗinmu ya faɗa? Za ka so a ce kai ne abun nan ya faru da kai? Ka manta ma'aiki SAW ya ce ka so wa ɗan uwanka abin da ka so wa kanka? Me ya sa ba ka so ma Annur abin da kai za ka so wa kanka ba?" Ya yi shiru daga nan, sanadiyyar kukan da ya ji ya zo masa. "Alhaji ji nake kana masa magana tamkar kana tsoronsa. Shin kana nufin ka masa nasiha kenan kawai mu ci gaba da rayuwa da shi? Impossible! Rayuwarsa a gidan pharm. IA ta zo ƙarshe. In fact, rayuwarsa aduniyar ma ta zo ƙarshe, matuƙar bai gano min ɗana ba." "Ku yafe min Dady..." Abin da ya iya faɗa kenan, duk da cewa akwai tarin maganganu a bakinsa. Sai dai kuka ba zai iya barinsa faɗarsu ba. Tashin hankalin da yake a yanzu fatar mutuwa ta zo ta ɗauke sa kawai yake yi. "Laifin da ka aikata Salman, laifi ne mai wahalar a yafe maka. Laifi ne da ba kai tsaye za a iya yafe wa mutum shi ba. Ka aikata babban zunubi Salman. Wallahi ban san me zan yi da kai ba. In yafe maka ka tafi ka bar gidan nan, ko kuwa in tirsasa ka sai ka gano inda Annur ɗinmu yake?" Hanan da Janan ne suka iso a daidai lokacin. Cikin kuka Hanan ta ce, "Ko ɗaya Dady." Ta ƙarisa isowa daf da su, ta rusuna tare da riƙe hannun Dadyn. "Dady idan har kuka kore shi, shi kansa bai san inda zai nufa ba. Mu duka ba mu san a rayuwar da zai faɗa ba. A baya ya yi yaudara ya zo gidan nan da zama ne saboda rashin madosar rayuwa, a sadda ma yake da Farouk Sardauna kenan. To Dady yanzu babu Farouk Sardauna, kuma an kore shi daga nan, wane hali kuke tunanin zai faɗa? Ba ku ganin kamar zai iya aikata abin da ya fi wanda ya yi a nan ma muni...?" Momy ta katse ta. "Ko ma gidan uban wa zai je sai dai ya je. Amma tabbas yau ne ƙarshen zamansa a gidan nan. Dole ya gano min ɗana, sannan kuma ya tafi uwa duniya ma ban damu ba." Janan ta doɗe ma Momy baki. "Haba Momy. Da bakinki kike faɗar wani ya tafi uwa duniya? Ashe ɗa ya fi ɗa kenan. Kina jin haushi saboda an ma Uncle Noor kurciya ya tafi ba a san inda yake ba, sannan kuma ke ma ga shi kina son wani ya tafi uwa duniyar." "Janan ramuwar gayya ce zan yi. Shi ma ya ɗanɗani yadda Annur ɗina ya ji. Ya ɗanɗani daɗi ko rashin daɗin yawon duniya." Janan ta gyaɗa kai. "Momy kar tashin hankali ya sa ki aikata abin da bai kamata ki aikata shi ba. Ban san haka zuciyarki take ba. Ni zuciyar Momy da na sani sassanya ce mai sauƙin hali. Tana da tausayi da jin-ƙan mutane." "Surutanku duk ba za su yi tasiri a gare ni ba. Kai!" Ta gwada wa Salman ƙofa. "Maza tashi ka tafi ɗakin Annur ka harhaɗa duk tsummokaranka. Na ba ka nan da sha-biyu na rana ka kammala komai, yanzun nan zan kira ƴan sanda su bi ka ka nemo min yarona. Idan suka ga za ka ba su matsala su tafi Office da kai, su maka tsinannen duka, in ma mutuwa za ka yi ka mutu ni ba ni da damuwa." Ya yi kneel down, hannuwansa tallabe da ƙeyarsa, yana kuka sosai mai sauti, ya ce, "Har ga Allah ban ga laifinki ba Momy, ba kuma zan taɓa gani ba. Sai dai zan miki rantsuwar ɗan musulmi, wallahi thumma tallahi na tuba, Allah kuma shi ne shaidana. Sannan kuma ban san inda Annur yake ba, wallahi." "Wa za ka marairaice mawa? Ba zan taɓa tausaya maka ba, tunda dai kai mugu ne, ka kasa tausaya wa bawan Allah. Mahaukaci amma kai har ka ga abun ka ci amanarsa, ka ha'ince shi." "Babu komai Momy zan tafi. Sai dai don Allah ina mai neman gafararku ke da Dady a bisa yaudararku da na yi. Ku yafe min ko zan samu rabauta a wurin Allah. Na sadaƙas, ko yanzu ki kira ƴan sanda su tafi da ni, don ban san inda zan gano Annur ba." "Ko ba ka faɗa ba zan kira su. Ka tashi ka ɓace min daga gani. Idan ka ga dama ka gudu kafin ƴan sandan su zo." Jiki ba ƙwari haka Sans ya tashi, Hanan ta riƙo ƙafar wandonsa tana kuka sosai. Tausayinsa take ji. Me ya sa Momy za ta kasa tausaya masa? Wannan wace irin zuciya ce wacce ba ta yafiya? A hankali ya sa hannu ya cire hannunta daga riƙon ƙafar wandonsa da ta yi, ya tafi yana waigen Dady, sai dai kan Dadyn sunkuye yake a ƙasa, yana zubar da ƙwalla. Kai tsaye ɗakinsa ya nufa. Rijif ya faɗi ƙasa, ya yi kneel down a bakin gado, kansa a bisa gadon sai hannuwansa ya miƙar da su ma a jikin gadon. "Ya Allah ka gaggauta ɗaukar rayuwata. Allah ka sani, na fi son mutuwa ta ɗauke ni a daidai wannan lokacin, ya Allah ka kawo min mutuwa ta zo ta tafi da ni..." Ya ci gaba da kuka sosai. A ɗaki kuwa sosai Hanan da Janan ke rarrasar Momy amma ta kartake lallai sai ta kira ƴan sanda. Dady ma duk da yana jin tausayin sans ɗin, yana kuma tunowa da alƙawarin da ya masa a asibitin India, amma takaicinsa da yake ji a yanzu sai ya ji sam! Ba zai iya cika masa alƙawarin ba. Ko ba komai yana ƙaunar ɗansa Annur, kuma ga shi Sans ne silar da suka rasa shi, rashin da suka gwammaci a kawo musu gawarshi ma afiye da zama inda ba su san ya yake ciki ba. Har wani irin zazzaɓi yake ji yana sauko masa. Cikin ƙarfin hali Hanan ta ce, "Dady ka taso ku karya, ka ga har kusan goma da rabi." "Ba na jin zan iya cin komai Hanan." Ta dawo kusa da shi. "Dole za ka ji yunwa Dady. Ba na so wannan tashin hankalin ya hana ka cin abinci. Ka ga kana da ulcer." Ta juya ga Momy. "Please momy go and have your break fast." "Hanan ba zan iya cin komai ba. Ku je kawai ku ku karya." Duk yadda Hanan ta yi da su a kan su zo su karya ɗin ƙi suka yi. Hakan ya sa su ɗin ma suka kasa cin komai. Sai kawai ta je dining ɗin, ta ɗauko ƴar launch box daga cikin dining carbinate. Ta zuba soyayyen ƙwai a ciki sannan ta ɗauki bredi guda ta ɗora a kai. Ta ɗauki flask da cup da spoon ta haɗa wuri guda, sannan ta shiga kitchen ta ɗauko ƙaramin basket. Jera kayan ta yi a ciki, ta ɗora container ɗin madara da sugar da milo, sannan ta nufi barin falon. Ji ta yi Momy ta ƙwala mata kira. "Ina za ki je da kaya?" Babu ko shakka bare tsoro ta ce, "Zan kai ma Uncle Salman ne." Ta taɓe baki. "Ba zan hana ki ba shi abincin ƙarshe na gidan nan ba. Ki kai masa, sannan ki ƙara ba shi tabbacin ƴan sanda na daf da zuwa su tafi da shi." Ba ta ko jira ta ƙarisa maganar ba ta ficewarta zuwa ɗakin Sans. Ta same shi a yadda ya shiga tun ɗazu sai famar kuka yake. Fuskarsa ta gama kumburewa, ta tako kusa da shi bayan ta ajje kwandon. "Uncle Salman..." Ya ɗago kansa cikin mamaki ya kalle ta. Ta zauna kusa da shi cike da tausayinsa. "Ka ɗauka cewa wannan ƙaddararka ce. Rubutaccen al'amari ba ya taɓa kauce wa mutum. Ba na so damuwa ta saka ka komawa ƴar gidan jiya. Ka yi attempting kashe kanka ko kuma ka koma harkar shaye-shaye. Don Allah ka cire komai a ranka. Insha Allahu Allah zai bayyana Uncle Noor, zai dawo ku ci gaba da rayuwa tare, tunda ka riga da ka saba da zama a nan." "Kayya! Hanan me ya yi saura a rayuwata? Farin-ciki ya daɗe da ƙaurace min. Tashin hankali kawai nake fuskanta. Mutuwa kawai nake..." Ta dafe masa baki. "Don Allah ka daina mana Uncle Salman. Ko da ƴan sandan sun zo sun tafi da kai na tabbatar da Dady zai fitar da kai. Ba zai juri ganinka a wurin ƴan sandan ba. Banda ma abun Momy, in nice ita ai ci gaba zan yi da zama da kai ko don sabon da muka yi. Ga kuma tsabar kama da kuka yi da Uncle Noor ɗin. Da kawai sai mu ci gaba da addua Allah ya bayyana mana shi. Tunda dai ƙaddara ta riga fata, mai faruwa ta riga da ta faru." Ya gyaɗa kansa cikin kuka. "Ka tashi ka karya please, ga kalaci nan na haɗa maka. Ta ce wai ƴan sandan za su zo. Amma da yardar Allah komai zai zo da sauƙi." Ta tashi ta tafi. Momy kuwa sake kiran ɗan sandan da mijin Islam ya turo mata lambarsa ta yi. Ya ba ta haƙuri cewa wani case ne suka tsaya handling, amma sun gama yanzu za su taso. Ta kashe wayar tana faɗin sai sun zo, tunda already ta musu text na address ɗin gidan. Janan da ke zaune ta rafka uban tagumi ta ce, "Momy ashe haka kike da kafiya?" Hanan ta harare ta daidai sadda ta iso ɗakin. Ita kam ta ƙudira cewa ba za ta sake tada ma Momy maganar ba, tunda dai ita ba ta san me kalmar haƙuri ke nufi ba. Ta je ta zuba wa maigadi kalacinsa ta kai masa da na mai gyaran flowers, sannan ta haɗo nata ita ma. Zama ta yi ta ci ta ƙoshi, ta gyara wurin sosai. Ƙarfe ɗaya da minti biyar wayar Dady ta yi ƙara. Kamar ba zai ɗauka ba dai ya daure ya duba, sai ya ga abokinsa ne ke kiransa. Gyara muryarsa ya yi saboda disashewar da ta fara yi. Ya kara wayar a kunnensa. "To, da wuri haka? Allah ya iso da kai lafiya. Ka yi amfani da address ɗin da na turo maka, babu wahalar ganewa gidan." Ya tsinke wayar. A daidai lokacin kuma mai gadi ya iso ɗakin, cewa ga ƴan sanda can har mutum uku sun zo. Momy ta gaggauta miƙewa, ko mayafi ba ta tsaya nema ba ta bi bayan mai gadin. Sai a nan hankalin Dady ya ƙara tashi. Yana ji a ranshi bai kyauta ba. Tabbas ya zama munafuki, saboda rashin cika alƙawari, kuma an siffanta mara cika alƙawari a cikin munafukai. Sai ya tashi ya bi bayan Momy, Hanan da Janan suka bi bayansa. Duk da halin rawar kai irin na Janan, sai ma ta fi Hanan ɗin damuwa. Take jin tashin hankali sosai bisa ga wannan al'amari. Gaban ƴan sandan Momy ta isa, ta gwada musu ɗakin Sans cewa su shiga su fito da shi. Babu musu kuwa suka shiga ɗin. Zaune yake ya tasa kwandon kayan kalacin a gabansa, bai fiddo komai ba sai haɗa kansa da guiwa da ya yi, ya yi shiru sai zancen zuci yake yi. Bai ji ƙarar shigowarsu ba sai muryar ɗaya daga cikinsu da ya ji ya ce, "Hajiya ta ba mu umurnin shigowa mu tafi da kai. Bisa ga babban laifi ba ƙarami ba. Za mu tafi da kai domin ka amsa wasu tambayoyi." Bai ko musa musu ba ya miƙe, saboda dama abin da yake zaman jira kenan tun ɗazu. Ya bi bayansu. A daidai gaban Momy da Dady ya rusuna. Cikin muryar kuka ya ce, "Momy, Dady, please ku gafarta min. Na sani ni mai laifi ne a gare ku. Da ba ni da bakin wanke kaina tunda dai na aikata ɗin. Ba zan taɓa mantawa da halarcinku ba. Ba zan taɓa mantawa da karamcinku ba." Ya duƙe a nan, yana kuka sosai. Horn suka ji, hakan ya sa suka waiga ga ƴar ƙaramar ƙofar jikin gate ɗin suna kallo. Da hanzari mai gadi ya buɗe masa gate ɗin, saboda tun fitowar Dady ya masa bayanin baƙon da zai zo ɗin. Yana shigowa ya masa nuni da parking space, ya faka motar tasa sannan ya fito. Dady ya ƙoƙarta dawo da walwalarsa, ya isa gare shi cikin murmushi yana faɗin, "Young Dr. Ji nake kamar a mafarki, yau ga ni ga ka." Ƙam-ƙam suka riƙe hannuwan junansu. Daidai sadda ƴan sandan suka ɗago Sans domin tafiya da shi, daidai lokacin ne baƙon ya haɗa ido da shi. Cikin mamaki ya sake darara idonshi. Ya ce, "Wani nake gani kamar Annur da na baro yanzu." Cike da mamaki Dady ya ce, "Annur kuma? A ina ka gan shi?" "Yanzun nan fa na baro shi gidan kawunsa, har na duba shi ba shi da lafiya." Ya riƙo hannun Sans bayan ƴan sanda sun miƙar da shi. "Annur nan ka kaɗo kuma? Ina Maryamar? Wani abu ya faru ne na ga ƴan sanda za su tafi da kai?" Momy ta kalle shi. Dady ya ce, "Dr. Wannan fa tun ɗazu muke nan tare da shi, in fact, a nan ma ya kwana. Ba na faɗa maka jiya muka dawo daga India ba? To ai shi ne Annur ɗin da na faɗa maka ba shi da lafiya ɗin." Kai ya kaɗa. "Akwai dai alamar tambaya. Kodai ƴan biyu ne?" Sai a nan Momy ta samu damar magana. "Dr. Hamdan a ina ka ga Annur ɗin?" "Gidan kawunshi mana. Baccin ma na tsaya shan mai ai da sai in ce muku yanzun nan muka rabu da shi..." Bai gama rufe baki ba. Su Maryama suka shigo. Uncle Marwan gaba, Yamaira biye da shi ta riƙo hannun Yesmeen, sai Maryama da Annur jere da juna. Dukkansu suka ɗaga kawanansu suna bin su da kallo, musamman ma Momy da ta saki baki tana bin annur da ido. Cikin murmushi Dr. Hamdan ya ce, "Haba! Ni fa in ce. Annur da alama dai ku ƴan biyu ne ko? Anyways, nan kuka yo kenan. To ga ɗan uwanka mai kama da kai nan ƴan sanda za su tafi da shi." Ko a jikinsa ya yi wannan maganar. Dama halinsa kenan. Da sauri cike da mamaki Annur ya isa ga Sans suka rungumi juna, dukkaninsu kuka suke yi sosai, suna jin soyayyar junansu na shiga duk wata kusurwar jiki da zukatansu. Ɗan uwa rabin jiki! Sai ma suka kasa rabuwa, bugun zukatansu na tafiya a tare, kamar yadda ruwan hawayensu ke zuba a kafaɗun junansu a tare. *** *Bari in dakata a nan yau dai kam. Na gaji. Ba laifi kusan 4k words na yi, kuma a zama ɗaya kawai.* *Sannunmu dai da jimirin yin comments. Haƙiƙa kuna faranta min rai sosai, inaa jin daɗin hakan. Khairat ta RAZ NOVELLA na gaishe ki. Na ji daɗin kiran da kika yi min tare da nuna farin-ciki da ƙaunarki ga ANS.* *Masoyana na nesa da na kusa, duk ina jin saƙon gaisuwa da jinjinar ku. Ina matuƙar jin daɗi da hakan. Allahi ya bar zumunci, ya ba mu ikon amfanuwa da darussan cikin labarin.* *Da alama dai saura ƙiris mu kawo gangara. Kaɗan ya rage in kammala warware ƙullallun abubuwa. Ku dai juri bibiyar alƙalamin Amrah, da sannu komai zai zo muku yadda kuke so.* *Da gaske saura ƙiris in zubda ma Sans ƙwalla. Sai dai kuma ya za a yi. Dole Momy ta jajirce don ganin ta ƙwatar wa ɗanta fansa. Domin kuwa aika-aika irin wacce Sans ya yi, ba abu mai sauƙin a yafe ta ba ne.* Thanks all. Pinky durling💞 RAZ 2 [9/27, 10:18 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taɓa zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 7⃣3⃣ Wattpad: PrincessAmrah *** Dukkansu babu wanda ya san sadda ƴan sandan suka tafi. Momy ce ta lallaɓa ta musu alama kan su tafi ɗin. Cike da mamaki Dady ke kallon yadda Annur da Sans suka kasa rabuwa da junansu. Hanan da Janan sai murmushi suke saki, duk da cewa su ɗin ma suna al'ajabin wannan tsananin kama da take tsakanin Annur da Sans. Uncle Marwan ne ya ce, "Duka sai mu rankaya cikin gida, zan mana bayanin duk yadda abubuwan suka kasance." Yawu ta haɗiya da ƙarfi Momy. Cikin ƙarfin hali ta matso magana, ta ce, "Alhaji Marwan kana nufin dama can ka san inda Annur ɗina yake? Me ya sa za ka ɓoye mana?" Ya yi murmushi. "Duka wannan tambayoyi ne da zan amsa mana su idan mun samu wuri mun zauna. Ga kuma Dr. A tsaye." Ya isa ga Dr. Hamdan yana murmushi. "Ashe dama nan za ka yo Dr." Dr. Hamdan ya murmusa. "Shi ne mutumin da na faɗa maka na zo wurinsa ɗin. Da alama ma dai kun san juna." Dady ya ce, "Young Dr. Ana ma maganar sanin juna ni da Marwana? Ƙanina ne uwarmu ɗaya ubanmu ɗaya." Da mamaki Dr. Hamdan ya kuma sakin murmushi. "Allah mai iko! Kuma fa daga gidansa nake yanzu mai kawai na biya na shawo. Ai ni ban ma sani ba." "Mu shiga daga ciki ko?" Dady ya faɗa cikin murmushin ƙarfin hali. Sai a sannan Annur da Sans suka saki juna. Yamaira ta riƙe musu hannuwa su duka biyun bayan ta saki hannun Yesmeen. Maryama kuma ta kama wa Yesmeen ɗin hannu, tana jin tsananin daɗi a duniyarta. Duk wata fargaba da damuwa da take a cikinta sai ta neme ta ta rasa. Sun kama hanyar babban falon gidan kenan Dr. Islam ta iso. Da sauri ta taddo su, saboda tunda Baban Abdul ya faɗa mata Momy na neman ƴan sanda hankalinta ya tashi. Tana asibiti ne ta duba wasu patients shi ya sa tun ɗazu ba ta zo ba. Ba ta ga fuskokin kowa ba sai Maryama da ta waigo tana kallon ta. Murmushi suka sakar wa juna, duk da yake cewa Islam mamakin mutanen da ta gani a gabanta take yi. Jira ta yi har ta ƙariso kusa da ita. Suka gaisa cikin sakin fuska sannan suka isa cikin falon. Take mamaki ya kama Islam ganin mai irin fuskar Annur har guda biyu sun zauna kusa da juna. Sai ta saki wayar hannunta ido buɗe ta kasa zama sai bin su da kallo take yi. Babu wanda ya mata bayani, har sai da ta jiyo muryar Momy cikin kuka ta ce, "Alhaji Marwana ka mana bayanin abin da yake faruwa, don Allah. Ka sa hankalina ya daɗa tashi, gabana ya ƙi ya daina faɗuwa." Alhaji Marwan ya yi gyaran murya. "Zan fara da yi mana wata ƴar guntuwar nasiha, game da ɗaukar ƙaddara kyakkyawa da mummuna. Duk abin da ka ga Allah ya tsara ga bayinSa to ka ɗauka cewa dole sai ya faru da su ɗin, duk dabararsu kuwa. Sannan sau da dama abin da ba ka tunanin faruwarsa sai ya faru. Abin da kake da tabbacin zai faru kuwa sai ka ga bai faru ɗin ba. Ina so ku ɗauka cewa dama can Allah ya ƙaddara cewa za ku raini Annur tun yarintarsa har ya girma, sannan kuma a ƙarshe ku samu labarin cewa ba ɗanku ba ne na asali, ba ku ne kuka haife shi ba." Daga Dady har Momy sai suka miƙe tsaye idanuwansu a buɗe suna bin Uncle Marwan da kallo. "Yaya Iqra ku koma ku zauna. Yanzun nan zan warware muku zare da abawa." Dady ne ya koma ya zauna, amma Momy ta gagara zama, Islam ma ta yi tsaye har yanzu ba ta daina mamaki ba. "Annur ba ɗanku ba ne. Duk ma yadda za a yi to tabbas ba shi ne ainahin ɗanku ba. Ta yiwu a asibitin da aka haife shi ne aka samu matsala aka sauya muku shi. Amma tabbas ɗan uwan Salman ne ga shi nan, ɗan uwan tagwaicinsa. Sannan kuma Yaya ga Yamaira matata ga ta." Ya nuna musu Yamairah da ta sunkuyar da kanta ƙasa tana kuka. "Kar ka faɗa mana magana son ranka Alhaji Marwan. Ni na haifi Annur da kaina fa. Ta ya za ka ce wai ba shi ne ɗana ba? Wace hujja gare ka ta cewa an sauya min shi ne?" "Ba ni da hujjar da zan yi proving zancen nan a yanzu, har sai mun je asibiti an yi gwajin DNA. Amma ina so na miki wata tambaya." Bai jira ta kuma cewa komai ba ya ci gaba, "Kin taɓa ganin mutane masu tsantsar kama irin ta Annur da Sans kuma suka kasance ba identical twince ba? Sadda kika haifi Annur ƴan biyu kika haifa aka ce miki kin rasa ɗaya? Salman da Yamaira ƴan Borno ne. A Borno State ke ma kika haihu. Bakya tunanin duk abin da na faɗa zai iya zama possible? I want you to think well, Hajiya Suhaila. Kafin mu je asibiti a muku DNA test." Dady ya ɗan fara gasgata zancen Alhaji Marwan. Sai ya dafe kansa yana kuka sosai, tamkar ba namiji ba. Shi dama can haka yake da zuciya mai rauni, ƙaramin abu ma sai ya saka shi zubda ƙwallarsa. Bai gama tunani ba ya ji muryar Dr. Hamdan ya ce, "Yanzu the best solution is that, a yi DNA test ɗin kamar yadda Alhaji Marwana ya faɗa. After that, idan za ku iya to tabbas za ku koma asibitin da aka haifi Annur. Akwai records na komai da ya faru in dai ba za ku iya manta date ɗin haihuwarsa ba. A lokacin har sunan nurse ɗin da ta karɓi haihuwarsa ma ana rubutawa. Sai ku zanta da ita. Ta yiwu a daidai lokacin da aka haife shi an haifi twince, sai aka musanya guda ɗin da ɗan da kuka haifa, aka damƙa muku Annur." Cikin kuka Yamairah ta ce, "Babu ko tantama abin da ya faru kenan. Mahaifiyarmu ta faɗa mana cewa ƴan biyu ne ta haifi Yaya Salman, amma ɗayan ya rasu a take." Sai Momy ta ƙwalalo ido haɗe da zubewa ƙasa rijif. Lokacin da ta haihu ta tuna. Shereefa da ta haihu aka ce mata ɗayan ya rasu. Cikin kuka ta ce, "Ya sunan mahaifiyar taku?" Yamaira ta ce, "Sunanta Shereefah." Momy ta dafe zuciyarta. Tana ganin yiuwar abin da a tunanin ta ba zai taɓa yiuwa ba. Kafin ta ce komai, Alhaji Marwan ya ce su taso su biyar; Dady, Momy, Annur, Sans da kuma Yamairah su tafi asibiti yanzun nan a yi ta ta ƙare. Yana so ya fitar da su Momy daga wasi-wasi. Dr. Hamdan ma ya miƙe cewa zai koma Kano yau. Amma Dady ya roƙe shi alfarmar ya jira su dawo. Ko gaisawar kirki ma ba su samu sun yi ba saboda wannan tashin hankalin. Zaman kuwa ya yi, Maryama da Isam sai kallon-kallo suke, sun kasa cewa ko uffan. Zaman tsit ne ya biyo ɗakin, sai ɓuruntun Hanan da ke girki a kitchen. Yesmeen kuwa ta yi barci tun ɗazu tunda ba da ita suka tafi ba. Dr. Hamdan latsar wayarsa kawai yake yi, sai ya ɗan nisa ya ce musu sannu. A asibiti kuwa, bayan an gama duka aka tabbatar wa su Momy cewa Annur ba jininsu ba ne, amma shi, Salman da kuma Yamairah jini ɗaya ne. Hakan ya daɗa tayar musu da hankali. Momy kamar zuciyarta za ta buga haka take ji. Ta rasa yadda aka yi hakan ta kasance. Wane irin daƙiƙanci da rashin hankali ne zai saka ma'aikaciyar asibiti tafka irin wannan babban kuskuren? A cikin mota kuka kawai Momy ke yi. Dady kuwa kukan zuci yake yi, wanda ya fi na hawaye ciwo. Alhaji Marwan da ke tuƙi ne ke ta tausarsu. "Shi ya sa kafin na tinkare ku da maganar, sai da na muku nasiha saboda na tabbata sai haka ta faru. Na sani, cewa babu daɗi, kuma dole za ku damu. Amma dole ku daure, ku miƙa komai ga Allah, sannan kuma ku miyar da komai ba komai ba..." Bai rufe baki ba Annur ya ce, "Kuma hakan ba wai yana nufin zan bar su Momy ba ne. Ko da a ce iyayena suna raye, na tabbata su kansu ba za su taɓa raba ni da su Momy ba. Raba ni da su kuwa tamkar raba ni da numfashina ne. Sun min abin da ba zan taɓa mantawa da su ba. Matar da ta shayar da ni, ta raine ni irin rainon da mahaifiya ke yi ga ɗan da ta haifa, har kuna tunanin akwai ranar da zan iya butulce ma su Momy? Har abada!" Nannauyar ajiyar zuciya Momy ta sauke, duk da haka dai hawaye na zuba bisa kumcinta. Sans bai ce komai ba. Sai jinjina lamarin kawai yake yi. A ranshi yake tunanin ashe ɗan uwansa na jini ne ya wulaƙantar da rayuwarsa. Ashe dai da rabon zai sake haɗuwa da jininsa. Ga shi Allah ya haɗa shi da mutum har biyu, ko ma uku. Tunda dai Yamairah ma kanta ta ajje ƴa, kenan ita ma ta shiga sahun jininsu. Bai san sadda ya saki murmushi ba, murmushin da har sai da ya bayyana. A haka suka ƙarisa gida mai gadi ya buɗe musu gate suka shiga ciki da motarsu. Dukkansu jiki a saɓule suke banda Sans da Yamairah. Su kam daɗi ne ya turnuƙe zukatansu. A falo suka yi branching, yanayin fuskokinsu kawai ya sa duk ƴan ɗakin suka gasgata cewa DNA ɗin bai zo daidai da na su Momy ba. Hannu Dady ya miƙa wa Dr. Hamdan haɗe da sakin murmushin ƙarfin hali. "Dr. Mun bar ku da jira." "Babu komai ai. Ga shi har na yi sallah ma." "To masha Allahu. Abu dai ya tabbata Dr. Ashe Annur ba jininmu ba ne." Ya goge ƙwallar da ta zubo masa a daidai nan. Haɗe da dakatawa saboda nauyin maganar da ya ji. Dr. Hamdan ya ce, "Kar ka damu Oga. Haƙuri za ka yi, haka Allah ya tsara muku tun asali. Yanzu ka ga wani al'amari na Allah, inda za ka san cewa komai rubutacce ne, yaushe rabo na da kai? Shekara da shekaru muka rabu, ko a waya ba mu tare. Amma cikin iko da hikimar Allah, kamar wasa na gan ka a Facebook an sako min kai a People You May Know. Ina ganin sunan na ji daɗi sosai, ban gama tabbatar da kai ɗin ba ne har sai sadda muka yi magana da kai. To ka ɗauka cewa wannan ɗin ma dama can rubutacce ne." "Babu abin da ya fi damu na irin wulaƙancin da na ma Salman. Na ci mutuncinsa, na ci zarafinsa a kan ɗan uwansa. Ashe ni ban sani ba haukan banza nake, a kan ɗan uwansa ne nake masifar, ɗan uwanshi gudan jininsa..." Yaimaira ta gaggauta dakatar da Momy. "Ki daina faɗar haka please. Yadda kika ɗauki Yaya Annur to a yanzun ma haka nake fatar ki ci gaba da ɗaukarsa. Na tabbatar da shi ɗin ma a nashi ɓangaren haka ne. Tunda dai mun rasa iyayenmu, kuma ko suna rayen ma wane irin butulu ne shi da zai bar ku bayan rayuwar da ya yi a tare da ku?" Sai a sannan Islam ta yi magana. "Lallai maganar Uncle Marwan gaskiya ce. Cewa so da dama abin da ba ka taɓa tsammani ba yana faruwa. Ga shi nan dai, tunda muke a rayuwarmu ba mu taɓa kawo wa rayukanmu ba cewa Yah Noor ba shi ne ainahin ɗan su Momy ba." "To ina ɗan namu yake?" Momy ta tambaya cikin kuka. Ta ji muryar Dady ya ce, "Ina tunanin shi ne ya rasu." Cikin takaici Momy ta kalli Dady. "Ba na tunanin ɗanmu yana raye, kamar shi ne ya rasu sai aka macanza shi a matsayin ɗan uwan tagwaicin Salman." Ta dafe kanta. Kuka sosai ke sake zo mata. Tana jin takaicin rayuwarta. Komai ganinsa take tamkar a mafarki. Kamar za a bubbuga ta ta tashi daga barcin da take yi. Dr. Hamdan suka ji ya ce, "Kamar yadda na faɗa muku a farko, daurewa za ku yi ku shirya ku tafi Maiduguri. FMC ɗin tasu an dawo da ita nan cikin Maiduguri, da ma'aikatan nasu da duk wasu records da ke akwai, duk da dai ba na tunanin har yanzu za a iya samun nurse ɗin da ta karɓi haihuwar tasu tana aiki ba ta yi retire ba. Amma dai sanin nata yana da amfani, nemanta kuma ba zai yi wahala ba." Alhaji Marwan ya ce, "Wannan gaskiya ne. Kuma abin da ya kamata a yi kenan, wata ƙila ba za a rasa wani labari daga gare ta ba." Dady ya ce, "To gobe idan Allah ya kai mu sai mu tafi. Hausawa suka ce da zafi-zafi kan daki ƙarfe. Mu yi komai kan lokaci, ta yadda za mu gama a kan lokaci." "Haka ne. Pharm IA ni bari in kama hanya, yanzu insha Allahu." Hanan da ke daidai isowa wurin ta ce, "Uncle an fa gama abinci ta ya za ka tafi ba tare da ka ci ba? Ga shi can a dining na jera." Da fara'a ya ce, "Ɗebo ki kawo min a nan kawai in ci." Ta koma dining ɗin. Faten dankalin turawa da kaza ne ta zubo masa a plate, ta sako fork da spoon sannan ta kawo masa. Drink ta kawo masa ta dire a gabansa sannan ta juya ta tafi. "Wai ni kam Maryama, ban ma tambaye ki lafiyar ango ba. Wannan tashin hankali bai bar ni ba." Kallon juna Maryama da Annur suka yi suka sakar ma junansu murmushi. Sannan ta ja hannunta suka wuce ɗaki. A can ta labarta mata duk abubuwan da suka faru tun daga farko har ƙarshe. Islam ta fasa kuka. "Haƙiƙa Amrah haske ce, haka mahaifiyarta ma. Tun ina yarinya ni da Aunty Saddiqa muka ɗora wa Amrah da iyayenta karan tsana. Muka tsane su kasantuwarsu talakawa. Sai ga su ta dalilin Mahaifiyar Amrah komai ya bayyana. Yes, ita ce sila. Saboda inda ba ta ba ki labari ba da komai bai faru ba. Da a haka za a yita zama cikin duhu ba tare da su Momy sun gano cewa Yah Noor ba ɗansu ba ne. Sannan ke Maryama." Ta rungomo Maryama, ta ce, "Tabbas ke jaruma ce. Mace ce ta kirki wacce ta san me take yi. Allah ne kaɗai zai iya biyanki abin da kika aikata. Har kika iya daurewa kika auri mahaukaci, wanda ko ni nan ba zan iya ba. Insha Allahu zan je har gidan su Amrah in roƙi mahaifiyarta gafara, a kan abubuwan da na aikata mata ita da Amrah." Maryama ta yi murmushi cike da jin daɗi, ta ce, "Za kuma ta yafe miki. Na san halin Umma sosai, a wurinta Amrah ta gado kyawawan halaye." Sai bayan sallar la'asar sannan Dr. Hamdan ya tafi. Sun masa godiya sosai, har Maryama ma sai da ta masa. Ta yi mamakin mutumin, yadda Dr. Sandra ta mata bayanin matsayinsa da kuma iliminsa, amma a haka yake da irin wannan sakin fuskar. Annur da Sans kam sai suka kasa rabuwa. Daidai da sallah tare suka je masallaci. Labari kawai suke yi. Sans na daɗa neman gafararsa bisa ga abin da ya aikata masa. Sai a yanzu ma yake jin duk yadda abun ya faru. Murmushi kawai ya saki yana jin daɗi, saboda a ganinsa hakan ma alkhairi ne, tunda har ya gano ƴan uwansa na jini wanda bai san da su ba. Sannan kuma ya gane cewa iyayensa basa raye, ko ba komai zai musu addua. A falo suka samu Momy da Dady zaune. Fuskar Momy duk ta kumbure tsabar kuka. Duk ba ta da walwala sosai. A gabanta suka zauna a tare. Ta tsura musu idanuwa tana kallo. Sai yanzu take daɗa tabbatar da tsantsar kamannin da ke tsakaninsu. Bambancinsu ba wani mai yawa ba ne. Sai wanda ya ajje hankalinsa sosai sannan zai fahimta. "Momy murmushi fa ya kamata a ce mun same ki kina yi a daidai wannan lokacin. Ga yaranki sun ƙaru, sun zama ƴan biyu. Sannan kuma ga ƙanwarsu Yamaira. Ai idan ni ne ke dariya zan ta yi inta famar wagar baki." Dady ya yi dariya sosai. "Yo Annur idan taita wagar baki kuma ai sai a kai ta psychiatry a ce ba ta da lafiya." Sans ya ce, "A'a fa Dady. Murna ce kawai." Ba su bar wurin ba har sai da suka ga sun saka ta dariya sosai. Dady ya ce da Annur ya je ya ce ma Maryama ta fito su tafi har an fara kiran magrib. Annur ya ce a dai bari har su yi sallah sannan su tafi. A ɗaki kuwa Hanan da Janan sai famar zaulayar Maryama suke. Wai yau za ta amarce, saboda sun mata, wacce tun ga bikin ta so yi mata ita amma sai ba ta samu damar komawa washe garin bikin ba, saboda zuwan su Hanan. "Tunda dai komai ya bayyana, na tabbata a yau komai zai kammama." Harararta ta yi cikin wasa, "Ke don Allah Aunty Islam." "Yo ai gaskiya ce Maryam. Da gaske sai kin dage, don yayan can nawa da alama gwarzon namiji ne." Ta yi saurin doɗe kunnuwanta. "Ai ba na ma jin ki ni kam." "Ke dai kika sani. Na tabbata a zuciyarki kina nan kina ta shi min albarka. Amma don iyayi sai wani rufar kunnuwa kike..." Ba ta rufe baki ba wayarya ta yi ringing. Baban Abdul ne ke kira hakan ya sa ta gaggauta ɗauka. Ce mata ya yi ga shi nan a falo ta fito su tafi da sauri, saboda sai sun biya ta gidan iyayensa sun ɗauko Abdul da aka kai tun safe yini, kasantuwar har yanzu hutunsu bai ƙare ba. Tashi ta yi Maryama ma ta bi bayanta. Daga rakiyar su Islam sai Annur ya ce ita ma ta fito su wuce. Bayan ta ɗauko hijabinta sai da Dady ya musu nasiha sosai sannan ya ba shi makullin Corolla LE ɗinsa cewa ya mallaka masa ita. Tunda asalin tashin ita ce a hannun Sans, ba kuma za a iya karɓarta daga gare shi ba. Ta yi mamakin yadda ya iya gane gidan nasu babu ko ɓata lokaci, amma sai da suka fara biyawa ya musu siyayya. Suna isa gida mai gadi ya buɗe musu gate bayan ya tabbatar cewa su ne. Suka shiga ya faka a madaidaicin parking space ɗin gidan. Maƙale da juna suka iso bakin ƙofar. Faɗi take ya sake ta ta fiddo key daga jikarta amma ya ƙi sakinta. Da dabara ta samu ta fiddo ta miƙa masa. Kasa buɗewa ya yi dole sai da ta karɓa ta buɗe ɗin, suka ƙarisa ciki. Sallar isha'i ya fara jan su suka yi. Sannan ya ce da ita ta tashi su yi nafila, irin wacce amarya da ango ke yi. Tun a nan jikinta ya yi sanyi, sai ta ƙara tabbatar da zancen Dr. Islam, cewa ba zai ɗaga mata ƙafa ba yau. Tana so, tabbas. Saboda babu macen da za ta zauna tare da namiji a matsayin mijinta na tsawon wannan lokacin, kuma a ce ko yaya ne ba ta ji sha'awarsa ba. "Ɗauko plate a juye kazar nan. Ina jin yunwa." Ta harare shi. "Sai fa da Hanan ta ce maka ta kawo abinci ta yi tuwon semo da ɗanyar kuɓewa ka ce a'a. Shi ne kuma za ka ce wai kana jin yunwa?" Ya kama hannuwanta duka biyun ya saka a nashi. "Da gaske ina jin yunwa Maryam..." Ji ta yi wata irin kasala ta wanzu a jikinta. Yadda ya kira sunan nata dole jikinta ya yi sanyi, ga kuma yadda yake wasa da ƴan yatsunta, duk sai ta fara rasa nutsuwarta. Da ƙyar ta iya saita kanta. Ta ce, "Ina zuwa." Ta yi saurin zare hannuwanta daga cikin nashi. Ba ta jima ba sai ga ta ta dawo da plate sai cups guda biyu. Naman kazar ta juye a ciki, sannan ta zuzzuba musu lemukan a cups ɗin. Tana gamawa kuma sai ta yi shiru, ta saita idanuwanta a wuri guda tana kallo. Ganin haka ya sa Annur kamo ta ta dawo a jikinsa. "Tunanin me Mi_amor ke yi?" Samun kanta yi da jin kunyarsa. Ta rufe fuskarta tana murmushi. "Kawai na tuno wasu lokuta ne, da nake mana irin wannan zuba abincin, nake baka a baki da nufin ba ka da lafiya. Wai ashe dai ɗan bawan Allah'n nan kallo na yake ƙyar, lafiyarsa ƙalau." Ya haɗa fuskarsu tana gogar juna. "Ba kodayaushe ne nake da lafiya ba, kamar yadda na faɗa. Abun yakan kaɗo min ne. Tun daga ranar da Umma ta zo ne dai ban ƙara jin ciwon ba." "To na ji. Ka ce kana jin yunwa kuma ka tsaya zuba surutu." Ya janye fuskar tasa sannan ya taɓe baki. "Yunwar fa ba wata ta a zo a gani ba ce. Ko kalamanki kawai na ci gaba da saurara zan iya jin cikina ya cika." Dukan wasa ta kai masa. "Lallai ma mutumin nan. Dama ba yunwar kake ji ba." Ta ɗauko plate ɗin. A hankali suka rinƙa feeding junansu, suna yi suna kora lemu mai sanyi har suka ƙoshi. Kwashe kayan duka ta yi ta kai kitchen, sannan ta dawo ta fesa freshner, a take ɗakin ya gauraye da ƙamshi. "Yah Noor na bar ka lafiya. Ni zan kwanta." Ta doshi hanyar barin ɗakin. Ai ko bakin ƙofa ba ta isa ba ta ji shi ya damƙo ta. Bai ce mata komai ba sai ji ta yi ya ɗauke ta ɗaf kamar wata jinjira. Ta rinƙa mutsu-mutsu tana faɗin ya sauke ta amma ya yi kamar bai ji ta ba. Sai a tsakiyar gado ya dire ta. "Yarinya kin ma isa? Kin san irin dauriyar da na rinƙa yi a baya ina kwanciya da ke a gadon nan ba tare da wani abu ya haɗa mu ba? To yau duk sai na fanshe dauriyar da na yi a baya" Sai ta samu kanta da faɗuwar gaba. "Yah Noor please..." Bai ko jira ta ƙarisa zancen ba ya haɗa bakinsa da nata. A take lamurran suka fara sauyawa. Soyayya yake gwada mata wacce ya jima yana wa Amrarsa tanadinta. Shi kanshi ya yi mamakin kansa, bai taɓa tsammanin akwai macen da zai damƙa wa dukkanin soyayyarsa ba, sai ga shi a yau ya samu wannan tabbacin. Tun tana noƙewa har ta miƙa masa ragama tare da ba shi haɗin kai. Da asubah ya kunna side lamp. Kyakkyawar fuskarta ya ƙura wa idanuwa. Lallausan gashin kanta duk ya barbazu bisa fuskarta. Barci take yi sosai ga hawaye da ya bushe a fuskarta. Sai ya saki murmushi haɗe da dafa goshinta. "Allah ya yi miki albarka Maryam. Allah ya biya miki dukkanin buƙatunki. Na ba ki amanar rayuwata Maryama. Duk da cewa Amrah na nan a cikin zuciyata, kamar rubutun da aka zana a jikin dutse, wanda babu gogewa a gare shi. Hakan ba zai taɓa saka ni daina ƙaunarki ba. Kalmar Amrah nake so ba za ki sake jin ta a bakina ba, har abada! Daga yanzu sai dai kin rinƙa ji na ce MARYAMA NAKE SO!" Ya sauke hannunshi daga dafewar goshin da ya mata. Sannan ya nufi toilet ya yi wanka ya ɗauro alwalla. *** *Masu kuka ina fatar kuka ya ƙare😀. Yanzu kam na tabbata babu sauran ɓacin rai. Sai dai zuwa Maiduguri da su Dady za su yi, ko za su dace? Amsar na a shafin gaba, wanda daga shi sai na ƙarshe insha Allah.* *Finally, the long awaited day has come. Annur da kansa ya furta Maryama yake so. Ya haƙura da faɗin Amrah yake so, har ƙarshen rayuwarsa. Wa da wa suka ji daɗi? In ga hannuwanku sama...lol.* *Masu kirana, masu turo min saƙon waya duk ina godiya. Allah ya saka muku da alkhairi ya bar zumunci.* Thanks all. Pinky durling💞 RAZ 2 [9/28, 8:47 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taba zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 7⃣4⃣ Wattpad: PrincessAmrah *** A bisa stool ta zauna tana shafa mai. Ji ta yi ya ɗora fuskarsa bisa kafaɗarta, ya tsura mata idanuwa ta cikin mudubi. Kallon sa ta yi ita ma ta cikin mudubin haɗe da ɓata fuska cike da shagwaɓa. Ya janye fuskar tasa. "Daure min fuska ma za ki yi ko?" "Ehh mana." Ta saki kakkausan murmushi. Bai sake faɗin komai ba ya ji wayarsa na ƙara. Ya koma ya ɗauko ta daga bakin gado sannan ya yi recieving. "I'll be on my way now, Dady. Na tsaya karyawa ne." Ya juyo ya kalli Maryama. "Dady ne. Wai in hanzarta. Ashe ma a jirgi za mu tafi, kuma ƙarfe goma jirgin zai tashi. Ki ga ikon Allah, jiya-jiyan nan ashe Uncle Marwan ya je ya binciko kuma aka yi sa'a akwai jirgin da zai tashi zuwa Maiduguri ɗin yau." Maryama ta miƙe tsaye. "To kuma ko karyawa fa ba ka yi ba a hakan za ka tafi?" "To ya zan yi Baby? Pass 9 fa. Ni kaɗai ake jira har Uncle Marwan ma ya kai Yamairah, dayake tare za mu tafi da ita." "Ina zuwa to." Ta nufi ɗakinta. Cakes irin na leda ɗin nan ta ɗebo masa guda huɗu. Sai ta ɗauki lemo ta saka a ledar ta miƙa masa. "Ban yarda ka zauna da yunwa ba. Ga shi ka samu ka ci please. Sai yaushe za ku dawo?" Ya ce, "Ina tsammanin in dai mun samu yadda muke so to gobe ma mu juyo. Sai idan abun ya yi tsayi ne sai jibi, wanda ma ba mu fatar hakan." "To yanzu Yaya ya za a yi? Mugunta ma ba ta bari ka faɗa min yadda zan yi ba?" Ya mata hararar wasa. "Ashe ma dai mugunta." "Ehh mana." Ya taɓe baki. "Yadda zan yi da ke a me wai?" "Ka san fa ba zan iya kwana a gidan nan ni kaɗai ba. Ko in tafi gidanmu kawai?" Cikin shagwaɓa ta yi maganar. Ya jawo ta ya haɗa fuskokinsu wuri guda, har hancinansu na gogar na juna. "A hakan ne za ki tafi gida? Ji fa ko tsayuwar kirki ta gagare ki yi. Idan na je yanzu zan turo miki Hanan da Janan, tunda har da Momy za a tafi, dama bai kamata a bar su gidan su kaɗai ba. Kawai sai a rufe." Ta jinjina kanta. "Allah ya kawo su lafiya to." Turaren oud ta fesa masa sannan ta taka masa har parking space. Da kanta ta buɗe masa motar ya shiga sannan ta rufe. Har ya fice tana ɗaga masa hannu sannan ta juya zuwa cikin gidan. Zama ta yi bisa 3 seater ta runtse idanuwanta. Wani irin farin-ciki take ji yana sauka a duniyarta. Ashe haka aure yake da daɗi? Sai yanzu ta gasgata. Musamman ma dai mutum ya auri wanda yake so yake son sa. Sai ka ji tamkar babu yakai a duk duniyar ma. Ta sakar ma kanta murmushi bayan ta buɗe idanuwanta. Abubuwan da suka wanzu tsakaninta da Annur a daren jiya ne suka hau dawo mata a ka. Kunyar kanta ta ji, ta saka tafukan hannayenta ta kare fuskar, sannan ta miƙe domin gyaran gidan. Yana isa ya samu duk sun hallara shi kaɗai ake jira. Sai suka masa uzuri saboda sun san ango ne. Yadda ake bin sa da kallo bayan ya gaishe su kuma duk sai ya ji kunya. Sans ya dafa masa kafaɗa. "Ango ka sha ƙamshi." Ya faɗa ƙasa-ƙasa, yana sakin murmushi. A take kuma sai ya tuno da alƙawarin da Farouk Sardauna ya nemi ya cika masa, na cewa ya auri Maryama. Ga shi bai samu damar cika alƙawarin ba, amma ɗan uwansa ya cika masa. Ya kuma sakin murmushi da ya tuno wasu abubuwan da suka faru a tsakaninsa da Maryama. Ƙaunar da ya yi mata daga kallo ɗaya , yadda ya gagara fitar da ita daga zuciyarsa har sai da boka ya masa aiki a kanta. Sai kuma ya tuno ranar da ya je har ƙofar gidansu ɗin nan. "Yaya ina kwana?" Yamairah ta gaishe da Annur cikin ladabi. Dama tun isowarta suka gaisa da Sans cike da ƙaunar juna, tana jin yadda ƙaunarsa ta shiga zuciyarta a lokaci guda, duk sai ta ji kewar iyayenta ta ragu daga cikin zuciyarta. "Lafiya lau ƙanwata. Kin tashi lafiya?" "Alhamdulillah." "To madalla. Ina su Hanan ne?" Momy da ke daidai fitowa ta ce, "Suna ɗaki Annur. Ka iso kenan." Ya sosa ƙeyarsa. "Na samu isowa Momy. Dama cewa na yi ko za a tura su Hanan ne wurin Maryama? Na ga su ɗin ma bai kamata su zauna su kaɗai ba. Ga ta ita ma can ita kaɗai." "Ehh gaskiya bai kamata ba. Amma kana ga kamar babu takura a tura wa Maryama su?" Ya ɗaga mata kai. "To ai shi kenan. Kawai sai ka shiga ka sanar da su su shirya ɗin." Ƙarfe goma saura kwata suka rankaya zuwa Airport. Goma da minti biyar jirginsu ya tashi. Mintuna arba'in suka saukar da su a babban Airport ɗin garin Maiduguri. Taxi biyu suka tsayar drop. Dady ya ce da su FMC yake so a kai su. Kai tsaye aka nufi can ɗin da su. Bayan sun sauka suka sallame su, sannan suka rankaya zuwa cikin asibitin. Maternity suka nufa, a baki-baki su Dady suka zazzauna bisa benci. Sai Momy da Yamaira suka ƙarisa cikin labour room ɗin, ta baro Yesmeen wurin Babanta. Daga farko ba a bar su shiga ba, saboda labour room ba wurin shige-da-fice ba ne. Sai suka musu bayanin abin da yake tafe da su sannan suka shiga ciki. Inda ke da tarin takardu aka nufa da su. Momy ta faɗi exact date ɗin haihuwar su Annur, sannan aka hau bincikar takardun. Ba a wani sha wahala ba aka gano, tunda komai jere yake an saka tambarin shekarar a jiki. Files guda goma sha ɗaya ne ta ɗauko, alamun a ranar yara sha-ɗaya aka haifa kenan. A hankali aka ringa dudduba kowanne. Sai a na uku da buɗewa ta ga sunan shereefah a jiki. Dukkaninsu sai da gabansu ya faɗi a daidai lokacin. Aka duba sunan wacce ta karɓi haihiwar, sunanta Sister Feenah, amma an rubuta cewa har da taimakon Dr. Rita, kasantuwar ba nace guda ke karbar haihuwar ba. Kuma twince ne ta haifa amma a lokacin na farkon ya rasu. Aka ajje file ɗin daga gefe sannan aka ci gaba da neman na Momy. A na biyun ƙarshe aka ga nata sunan a jiki. Ita kuma Sister Rita ce ta karɓi haihuwarta da taimakon Sister Feenah. Matar da ke duba musu ta ce, "Sister Rita Stephen ce ta karɓi haihuwar. Sai dai kuma ta ɗan jima da yin retire gaskiya." Gaban momy ya faɗi. Ta ce, "Please ba ki san a inda za mu same ta ba?" Ta ɗan yi shiru jim! Kafin ta ce, "Ehh to, da dai na san tana da wata babbar chemist a kusa da asibitin da mijinta ya buɗe, dayake ko sadda asibitin nan take a Bama to ita gaskiya nan garin take aure, weekend ne dai take zuwa wurin mijinta, a yadda na ji labari. Amma yanzu ba zan ba ku tabbaci ba gaskiya, don na jima rabon da in ji wani labari a kanta ko kuma in gitta ta asibitin. Sai dai ko na rubuta muku address na asibitin, sai ku je ko za ku dace." Momy suka miƙe jiki a saɓule. Godiya suka ma matar bayan ta rubuta musu address ɗin a paper suka tafi. Suna fita duk su Dady suka mimmiƙe. Tambayarsu suke yi yadda ake ciki amma Momy ta ce musu babu nasara. An dai basu address na matar da ta karɓi haihuwar tasu, wata ƙila su dace. Dady ya ce, "Tunda dai mace ce. Dole ku za ku jagoranci komai. Kai Alhaji Marwana ku je ku sama mana Hotel, alah-bishi mu sai mu je neman nata da Suhailah da kuma Yamairah. Idan mun gama sai mu yi waya da ku mu same ku." Yamaira ta ce, "Dady mu banda mu ni da Momy. Na kira Ummi na faɗa mata ni zan sauka a gidanta, Momy kuma sai a turo driver daga gidan su Ummi ɗin a kai ta can ta kwana." "Babu damuwa dai ko?" Dady ya faɗa yana kallon Yamaira. "Babu damuwa insha Allahu." "To shi kenan ai. Annur ku tafi. Duk yadda ake ciki zan rinƙa kiranku a waya." Daga nan suka tsayar da abun hawa. Su Annur suka ce a kai su hotel mai kyau, Momy kuma ta faɗa wa dreban address na waccan asibitin sannan suka tafi. A gaban asibitin ya dire su. Daga gefensa suka hangi RS Pharmaceutical, hakan ya ba su tabbacin chemist ɗin ne na Rita. Suka sallami mai mota sannan suka taka zuwa cikin chemist ɗin. Babbar chemist ce, hakan ya sa take da maaikata a cikinta wanda aƙalla za su kai mutum huɗu. Sallama Dady ya yi sannan ya ba wani hannu suka gaisa kasantuwar ya ga alamun musulunci a tattare da shi, tafkeken tabon sallah da ke goshinsa, da kuma counter da ke maƙale a ƴar yatsarsa yana tasbihi. Amsa sallamar ya yi, Dady ya ce da shi suna tambaya ne. "Don Allah nan ne chemist ɗin Sister Rita Stephen, wata tsohuwar maaikaciyar FMC?" Matashin ya ce ehh nan ne, suna da buƙatar wani abu ne? Nannauyar ajiyar zuciya suka sauke su duka ukun. Momy ta yi saurin faɗin, "Don Allah a ina za mu same ta?" "Tana gidanta. Amma takan zo nan chemist ɗin a irin ranar yau. Bari na kira muku ita." "Godiya muke." Dady ya faɗa cikin murmushi. Bayan ya kira ta ta ɗauka. Yake tambayarta za ta samu zuwa yau kuwa? Ta ce da shi wani abun ne? Ya ba ta amsa da baƙi ne suka zo neman ta. Wayar ta ce ya ba baƙin ta ji ko su waye. Momy ta karɓa suka gaisa cikin sakin fuska. Ta mata bayani cewa ta taɓa karɓar haihuwarta ne, to wata magana take so su yi da ita. Cewa ta yi su jira ta a nan ga ta nan zuwa yanzu. Matashin mai suna Ibrahim ya basu wurin zama, sannan ya bayar aka siyo musu ruwan roba. Godiya sosai suka yi masa. An ɗauki kusan tsawon awa ɗaya sai ga Rita ta iso. Kallon ta Momy ta yi sosai. Tabbas ita ce. Kamanninta ba su sauya ba, sai dai dattijanta kawai da ta yi. Tana ganin Momy ta ƙwalalo ido tana mata kallon sani. Da hannu ta rinƙa gwada ta tana son ta tuno sunanta. Momy ta tare ta da faɗin, "Mrs. Suhaila IA..." "Ezactly" Rita ta faɗa haɗe da rungume Momy. Sai kuma kuka daga nan. Momy ta raba jikinsu tana tambayarta me take wa kuka? "Its a long story Suhaila. I did the wrong things to you. I dont thing you can forgive me." Cike da mamaki suke kallon ta. Ta ce da su su bi bayanta zuwa ƙuryar chemist ɗin, inda tarkacen kwalaye ne kawai a ciki. Cikin kuka ta ce, "I've been waiting for this day, ranar da Allah zai haɗa ni da ke, na faɗa miki wani ɓoyayyen al'amari da babu wanda ya san shi, daga ni, sai Sister Asabe sai kuma Alhaji Abubakar Abu Sardauna." Komawa baya. Bayan Suhaila ta haihu, yaron da ta haifa pre-tamp ne bai isa haihuwa ba. Sai ya zamanto ba shi da lafiyar kirki, har numfashinsa ma ba ya fita da kyau, da alama ma yana da pneumonia. Ita kuma Shereefa ta haifi yaro guda, kamar dai yadda labarin ya zo a baya. To bayan Nurse ɗin da ta karɓi duty daga hannun Rita ta tabbatar wa Suhaila cewa ga yaronta nan, ta ma yi mamakin yadda numfashin nasa ya koma daidai, kamar ma bai taba yin ciwon ba. Suhailah ta koma resting room, shi kuma ainahin yaron da ta haifa ɗin aka saka shi a kwali a tunanin Rita ya mutu. Ganin halin da Shereefa ke ciki na naƙuda, kawai sai Sister Asabe ta yi tunanin ta miƙa gawar yaron ga mahaifinsa, tunda yana waje zaune. Dubawar da za ta sake yi, sai ta ga yaro na fitar da numfashi sama-sama, alamar da bai mutu ba. A tsorace ta sake duba shi, nan ta sake tabbatar da cewa fa yaron yana da rai. Ba ta yarda ta faɗa wa kowa ba, tunda babu wanda ya gane cewa yaron da ran shi. Sai ta latsa kiran Alhaji Abubakar Abu Sardauna, bayan ta lelleƙa ta ga babu mai kallon ta. Yana ɗauka cikin murya ƙasa-ƙasa ta ce, "Alhaji where are you now?" Cikin muryar damuwa ya ce, "Sister ba mu da wani zaɓin da ya wuce mu tafi da gawar ƴarmu. Ga mu nan a gida yanzu haka ma mun iso, zan tattara mutane a yi shirin yi wa ƴarmu wanka a kai ta ƙabarinta." Ta sake lelleƙawa ta ga babu mai kallon ta. Ta ce, "In da hali ka dawo yanzu da gawar. Na samar maka yaro." Ya ƙwalalo ido cikin mamaki, kafin ya faɗi komai cikin hanzari ta zayyane masa yadda abin ya faru, cewa iyayensa sun yi zaton ya rasu. Kamar ba zai yi ba dai ya ce, "Sister bakya tunanin faruwar wani abu a gaba?" Ta ce, "Idan har ka ga wani abu ya faru to tabbas ba ka ba ni wadatattun kuɗi ba ne. Amma matuƙar ka bani, to tabbas maganar za ta kasance a lulluɓe. Tsakanina da Sister Rita da kai ne kawai, ita ma ɗin don ya zama dole sai ta ji, tunda dai ta san cewa ƴar da ka haifa mace ce, tunda kafin ta tafi ne kuka bar nan, sannan kuma ta san fuskar wannan jinjirin." Alhajin ya jinjina lamarin, sannan ya ce ga shi nan zuwa yanzu, amma ta yaya zai shigo da gawar yaron? Ta ce, "Abu ne mai sauƙi wannan, zan kira Rita yanzu. Idan ka iso dai just call me." Ya tsinke wayar. A ranta tana nazarin dukiyar da za ta samu ta wannan hanyar. Ta san tsawon lokacin da Alhajin ya ɗauka yana son haihuwa saboda unguwarsu guda. Sai ga shi Allah ya ba shi ita, kuma lokaci guda ƴar ta rasu. Ta yi murmushi sannan ta kira Rita a waya. Bayan Rita ta ɗauka ne ta mata bayanin abin da ke faruwa. Rita ta yi dariya, ta ce, "Sister Asabe kin fi ni son kuɗi fa." "Sister Rita to wa ya ƙi kuɗi? Yanzu dai ina so ki faɗa min yadda za a yi a shigo da gawar yarinyar, da kuma yadda za a fita da wannan jinjirin mai rai." Rita ta ce, "Bari in zo kawai. Zan zo da sisterna, na san me za a yi after that." Babu jimawa Rita ta iso ita da ƙanwarta da ta umurta ta ɗauko showel na goyo. Isar ta ta yi daidai da isar alhaji Abubakar. Sister Asabe ta haɗa su ta waya. Bayan Rita ta karbi gawar yarinyar, sai ta ba ƙanwar tata ita ta goya kamar mai rai, sannan ta laɓe daga nesa, ta ce da ita ta nufi labour room kai tsaye ta ce wurin Sister Asabe ta zo. Abin da ya faru ɗin kuwa kenan. Tana zuwa aka kai ta inda Asabe, ta ma wacce ke zaune wurin wayo ta tashi, sannan ta lelleƙa ta ga babu mai kallon ta. Ta fiddo yaron daga cikin kwali, wanda har yanzu bai daina fitar da numfashi sama-sama ba. Ta gaggauta saka gawar yarinyar a cikin kwalin, ta mata kwanciyar ruf da ciki wai don kar a gane cewa mace ce. Cikin rawar jiki yarinyar ta tafi, kallo guda za a mata a tabbatar cewa ba ta da gaskiya. Tun daga nesa Rita ta iso ga ƙanwar tata tana mata murmushi. Kai yarinyar ta ɗaga mata alamun sun yi nasara. A tare suka isa wurin Alhaji Abubakar. "Alhaji ga yaro. Amma sai ka hanzarta ka kai shi asibiti, saboda ba shi da wadatacciyar lafiya." Ya ce, "Zan kai shi private hospital a ba shi first aid, in ya so ya ji sauƙi sai na fidda shi waje." Ya buɗe dash board na motarsa. Kuɗi ne bandir na ƴan dubu dubu har guda uku. Ya miƙa wa Rita, ya ce nasu ne su kaɗai, zai sallami Asabe daga baya, tunda dai dama can ya san ta, sun taɓa zama a unguwa ɗaya. Suka masa godiya sannan ya tafi. Matarsa da ta karɓi yaron sai kallon sa take yi. Gawar wancan yaron kuma saboda tashin hankalin da mijinta Shereefar ya shiga, bai tsaya duba gawar ba kawai ya damƙa ta ga wani ɗan uwansa da ya zo, ya ce a sallaci yaron tunda an jima da haihuwarsa, shi zai tsaya nan har Shereefar ta ƙarisa haihuwa. Yadda abun ya kasance kenan, wato dai su kansu su shereefar ba ainahin ɗan Suhailah ba ne aka ba su. Mace ce ma ɗiyar wani mutumin na daban. Washe gari bayan Rita ta dawo aiki, take dudduba record na yaran da aka ɗora a gadon auna lafiya jiya. A nan ta ga sakamako, cewa yaron nan mai pneumonia shi ne asalin yaron Suhailah, saboda ta san cewa yaron Suhailar ne ta haifa pre-tamp, wanda har numfashinsa ba ya fita daidai, to kuma sakamakonsa shi ne ya yi daidai da wanda ke hannun Alhaji Abubakar sardauna. Shi kuma wanda aka rubuta sunan mahaifiyarsa Suhailar a ƙasa, lafiyayye ne, ga kuma hotonsa a jiki, shi ne asalin ɗan da Shereefa ta haifa. Ta dafe kanta tana tunanin mafita. Ita kanta ta san akwai kuskure cikin lamarin. Ta tabbatar cewa ainahin yaron da Shereefah ta haifa ne zai ci gaba da rayuwa a gidan Suhaila. Shi kuma na Suhailah da ta haifa, shi ne a hannun Alhaji Abubakar, sai aka ba Shereefa gawar ƴarsa a matsayin shi ne ɗanta da ya rasu. "Wannan shi ne ainahin abin da ya faru Mrs. Suhaila. Na jima ina neman inda zan haɗu da ke na roƙi gafararki. Su ma su Shereefa na neme su ban samu ba. Sannan kuma na tona asiri, kasantuwar nadanar da na yi, na tabbatar cewa ba mu aikata daidai ba. Son kuɗi da neman duniya ne kawai ya ja mana aikata wannan babban kuskure, sai ga shi kuɗin ko daɗewa ba su yi ba, banza da wofi suka ƙare." Ta ƙarisa maganar tana kuka sosai, kukan nadama. Ita kanta Momyn kukan take yi. Tana jinjina mummunan hali irin na Rita da Asabe. A kan dubu ɗari uku da wani abu ne suka yi wannan aika-aikar. Cikin kuka ta ce, "Ba ku kyauta ba Rita, ba ku mana adalci ba. Babu babban mugu kamar shi Alhaji Abubakar ɗin da ya karɓar mana yaro, bayan ga gidajen marayu can idan ya so zai iya zuwa ya karɓo yaro duk irin wanda yake so." Dady ya dafe kansa cikin jinjina lamarin. Ya ce, "Yanzu dai kenan yaronmu yana wurin Alhaji Abubakar Abu Sardauna." Rita ta ɗaga kanta tana kuka. "Please forgive me Alhaji. Na san ban kyauta ba, and I've regret it. Ku yafe min, don Allah ba don ni ba." Dady ya gyaɗa kansa. "Shi kenan ai, ya wuce sai mu tari gaba." "Na gode Sir. Bari na ba ku contact na Alhaji Abubakar. Zan fara kiransa na masa bayani, ku ma sai ku kira shi. Idan ya musa har kotu zan iya zuwa na fallasa shi, in ya so ni ma a kama ni, saboda na san ban aikata abun kirki ba, daga ni ɗin har Asabe." Ta zaro wayarta daga hand bag ta hau neman lambar tasa. "Har bayan wannan case ɗin mun yi waya da shi, saboda ya ji daɗin abin da muka masa ya karɓi lambata daga wurin Asabe. Sai dai bayan an yi kamar shekara biyu da faruwar abun, bai sake nema na ba, kamar yadda ni ma ɗin ban neme shi ba." Ta latsa kiran nasa. A kashe ta ji, hakan ya sa ta sake kira, nan ɗin ma dai ba ta samu ba. Dady ya ce, "Ba ni lambar tasa kawai, in ya so ko daga baya ne idan ya buɗe wayar sai ki sake kiransa. Ni ma zan yita gwadawa har a dace." Bayan ta ba shi lambar ne suka miƙe za su tafi. Sosai Momy ke jin haushin ta. Sai dai yadda ta ga babbar mace kamar ta ta dage rusar kuka tana musu magiya, har ƙasa ta duƙa tana roƙonsu su yafe mata. Hakan ya sa ta ce sun yafe mata ɗin. Da haka suka rabu, Yamairah dai ba uhm ba uhm uhm. Mamakin al'amarin kawai take yi. Shiru ya ratsa tsakaninsu har suka tsayar da taxi. Yamaira ta kwatanta masa gidan Ummi sannan suka tafi. Wayar Dady ce ta yi ƙara. Ko da ya duba sai ya ga Sans ne ke kiransa, kasantuwar Annur babu waya a hannunsa. Ya ɗauka cikin sassanyar murya. Sans ya tambaye shi yadda ake ciki, ce masa kawai ya yi "Ainahin ɗan namu wai yawa wurin wani mutumi Alhaji Abubakar Abu Sardauna." Cike da mamaki Sans ya miƙe tsaye, idanuwansa a buɗe. Ganin haka ya sa Uncle Marwan da Annur ma suka miƙe suna tambayarsa lafiya. Jin shiru ya sa Sans ya ce, "Ga ni nan zuwa dai zan muku bayanin komai. Ya sunan Hotel ɗin da kuka sauka ɗin?" Da ƙyar ya iya tattaro maganar ya faɗa wa Dady sunan Hotel ɗin, sannan ya kashe waya. Uncle Marwan ya ce, "Ba ka mana bayanin komai ba Salman." Sannan ya koma ya zauna. Ya ce, "Wai yaron yana wurin Alhaji Abubakar Abu Sardauna." "Subhanallahi! To garin yaya haka?" Annur ya ce, "Abun tambayar kenan Uncle." Sans ya ce, "Ba wannan nake wa mamaki ba." Duk suka tsura masa idanuwa. "Ina jin sunan nan a bakin Farouk Sardauna kafin ya rasu, wai Yayan babansa ne haka." "Banda abun ka Salman, ka sani ko sunan ne ya zo ɗaya?" Bobby ya ce, "Kuma Uncle sai duka sunayen a jere ya zamto guda? Baban Farouk ɗin ma kansa sunansa Alhaji Usman Abu Sardauna, amma Alhaji Usman Sardauna kawai ake ce masa." Ya kuma zaro idanuwa. "I can remember something. Cikin ciwon Farouk ya tsananta, na rinƙa jin wasu kalamai na fitowa daga bakin Dadynsa. Haka kuma bayan ya rasu ma, na ji shi yana cewa wai ya kasa cika alƙawarin da ya ɗaukar wa yayansa na riƙon Farouk yadda ya kamata, bai ba shi kyakkyawar tarbiyya ba." Duk suka bi shi da kallo. "Kuma na ji shi yana cewa wai Farouk ya bi mariƙinsa na ainahi inda ya tafi (lahira). Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Kar dai a ce Farouk ne ainahin ɗan da su Momy suka haifa." Annur ya ce, "Wanene Farouk Sardauna?" Sans ya ce, "Wani abokina ne da ya rasu. Wanda ya fara taimakona bayan na shigo garin Katsina." Uncle Marwan ya ce, "Yadda za a yi, idan kana da lambar wayar Alhaji Usman ɗin, sai Dadynku ya kira sa idan ya dawo. Saboda zai fi kamata a ce daga bakinsa maganar ta fito." Sans ya ce, "Ina da lambarsa Uncle. Lallai al'amarin Allah ba ya taɓa ƙarewa. Farouk Sardauna ɗan su Momy ne?" Alhaji Marwan ya ce, "Tukuna dai, ai ba mu gama tabbatarwa ba. Dalilin da ya sa na ce ka kira shi ɗin kenan. Idan muka ji daga bakinsa same da wannan, to sai mu tabbatar da komai, ka ga gobe sai mu juya zuwa Katsina. Idan kuma ba shi ɗin ba ne, dole mu bincika mu gano ainahin wanda ya karɓe shi ɗin, sannan ko muna tunanin tafiya." Annur ya riƙe haɓarsa, ya jinjina girman lamarin Ubangijinsa. Wayar Sans ce ta yi ƙara, sai ya yi zaton ko Dady ne, yana dubawa ya ga lamba ce da bai san ta ba. Da sallama ya ɗauka haɗe da karawa a kunnensa, muryar Maryama ya ji ta yi sallama, yana ji ya gane muryar tata. Tun ranar da ya baro gidansu ɗin nan dama ya goge lambarta daga cikin wayar tashi. "Mai miji, na dai san shi kika kira nema. Ga shi to." "Yaya Salman..." Ta faɗa cikin kunya. Shi ma Annur ɗin da kunyar Uncle Marwan ya gaggauta fita. Yana faɗin, "Ta kasa haƙura dole sai ta ji muryar mijinta." "Ah to ya son ranka. Dole na kira na ji lafiyar mai gidana. Na kuma ji da ƴan mata nawa ya yi magana yau?" Ya ɗora hannunsa a goshi alamar tunani. "Ina ji duka ba za su wuce goma sha biyar ba. Ai ban yi da yawa ba ko?" Ta harare shi tamkar yana kusa da ita ne. "Ai da sai in biyo ka da yammacin nan, in ji dalilinsu na kallar min miji har suka yi magana da shi." "Lallai ma yarinyar nan. Ba wannan ba. Ya lafiyar iyalina?" "Suna lafiya ƙalau. Ya gajiyar tafiya? Fatar dai an dace." Annur ya ɗan yi jim kaɗan, kafin ya ce, "Dady dai bai dawo ba tukuna, dayake mu muna hotel ne. Amma na ji shi yana waya da Salman, wai wani Farouk Sardauna shi ne asalin ɗan nasu..." Tun bai rufe baki ba Maryama ta jeho masa tambaya. "Wane Farouk Sardauna? Bobby dai da ya rasu wanda na sani?" "Ehh, shi fa. Don na ji Salman ya ce wai ya rasu. Amma dai ba mu gama tabbatarwa ba tukuna. Sai Dady ya dawo zai kira Baban Farouk ɗin su yi magana." Salati Maryama ta saki. "To garin ya wannan al'amari ya kasance?" "Allah masani Maryam. Sai dai ya dawo ɗin mu ji komai. Su Yamairah da Momy akwai inda za su kwana. Wai gidan su wata Ummi." "Allah sarki! To Allah ya jishe mu alkhairi. Ka gaishe min da su duka. Kuma don Allah ka ce da Yaya Salman wai ya biya ni lada, saboda na kusa tsamo shi daga sahun tuzurai." Ya ja murmushi. "Bakya gajiya da sokana. Mata kika samar masa?" "Ehh mana Yah Noor. Kuma ni da kai ma za mu je mu nema masa auren. Har na kira a waya na faɗa mata, ta kuma amince." "Hmm! To shi kenan. Ki gaishe da su Hanan." "Za su ji ƙwarai. Ba mu tare ni ina ɗakinka. Su kuma suna ɗakina." Ya saki murmushi. "Wato dai kin musu wayo kika tafi waya da mijinki." "To ai hakan shi ne daidai. Na tabbata kai ɗin ma ka baro wurin da su Yah Salman suke don ka yi waya da matarka." "Ba ki ji wallahi." Ya saki dariya. "Na san hanyar da zan bi in rama wannan tsokanar taki. Wannan bakin maganar shi zan magance." "Na ji dai." "To ya yi. Ki huta lafiya. Wata ƙila ma gobe za mu juyo." "Allah ya yarje mana. Sai anjima." Suka tsinke wayoyin. Sai bayan la'asar liƙis sannan Dady ya dawo, daf da magrib. Kallo guda za a masa a tabbatar da ba ya cikin nutsuwarsa. Bayan ya zauna ne ya musu bayanin duk abin da ya faru kamar yadda Rita ta sanar da su. "Na san halin da kuke ciki a yanzu dole za ku damu. Amma kalmar nan dai guda ba zan daina maimaita muku ita ba. Ku yi haƙuri ku kuma ƙara yin haƙuri ku ɗauki ƙaddara. Wannan al'amari dama can Allah ya tsara haka zai kasance. To sai mu taru mu rungumi ƙaddara. Mu kuma ɗauka cewa Annur da Salman Allah ya sauya mana da su ne a madadin..." Bai ƙarisa ba Dady ya ce, "Ai dama ba ta ce mana fa bai raye ba. Lambar mutumin dai tunda muka rabu da ita nake ta nema a kashe. Abin da ya ƙarisa kashe min jiki kenan. Gaskiya in har ban gano wannan mutumin ba, to lallai sai na shigar da Rita ƙara. Don ba zan lamunci wannan muguntar ba. An raba mu da gudan jininmu da gangan." Uncle Marwan ya gyaɗa masa kai. "Me ya sa za ka yi ƙarar ta? Kai da kanka kake faɗa mana irin kukan da take yi na nadama. Idan kuwa har ka yi ƙararta ai ba ka kyauta ba. Shi ya sa na ce maka ka ɗauki ƙaddara. Dama haka Allah ya tsara mana. Kuma..." Ya kwashi duk yadda suka yi ɗazu ya sanar da Dady. Cike da mamaki yake kallon Sans. "Me ya sa ka faɗi haka Salman?" Cikin girmamawa Sans ya ce, "Sunan ya zo iri ɗaya ne Dady. Baya ga haka kuma, tabbacin da na samu daga bakin Dadyn Farouk cewa ba ɗansa ba ne, sannan a ƙarshe ma ya ambaci ba ɗan yayan nashi ba ne, wai ɗan riƙonsa ne." Dady ya yi shiru zuciyarsa na duka da sauri da sauri. "Dama kai muke jira ka zo sai ka karɓi lambar Alhaji Usman ɗin ka kira sa da kanka ku yi magana. Ka ga ta nan za a samu tabbacin al'amarin." Dady ya jinjina kai sannan y karɓi wayar Sans ya rubuta lambar Dady ɗin ya latsa kiransa. Bayan ya ɗauka da sallama suka gaisa. Dady ya masa bayanin kansa sannan cikin faran-faran Dadyn Boby ya sake gaishe da Dady. "Wato Alhaji Usman wata ƴar matsala ce ta sa na kira ka..." Ya faɗa masa komai da ya faru. Kuka ya ji ya fasa bayyananne. Hakan ya sa Dady ya saka wayar a handsfree ta yadda duk za su jijji maganar. Ya ce, "Subhanallahi! Alhaji Usman lafiya?" "Dole na yi kuka Alhaji IA. Ashe da gaske zan ga iyayen Farouk na gaskiya?" Mamaki ya kama su su duka. "Na gaskiya? Kenan da gaske ɗan namu ne?" "Babu ko tantama Marigayi Farouk ɗanku ne. Domin kuwa ba Yaya Abubakar ne ya haife shi ba. Labarin yana da tsawo, sai dai zan taƙaita maka shi." Komawa baya Cikin wata irin murya mai nuna zallar tashin hankali yake magana. "Usman ciwon nan nawa da alamu ba na tashi ba ne. Wani irin abu nake ji da tunda nake a rayuwata ban taɓa jin irinsa ba. Don Allah ga amanar Farouk nan, ka kula da shi, tamkar yadda za ka kula da naka da za ka haifa da cikinka." "Ka daina faɗar haka Yaya Abubakar. Insha Allahu za ka tashi ka ci gaba da rayuwarka. Shi ciwo ai ba mutuwa ba ne." "Ko kaɗan ba na jin haka a jikina Usman. Ga amanar Farouk nan ɗan shekara uku. Don Allah ka kula da shi, ka ga yadda muka rabu da matata Safina, rabuwa mara daɗi, ashe ita kanta waccan yarinyar da ta haifa ba ƴata ba ce, wai maza take bi a waje. Sai da ciwon nan ya kama ni asirinta ya bayyana. Babu nadama ko kaɗan a tattare da ita kuma ta nemi saki na sake ta. Ba ta nemi tafiya da Farouk ba, don ta san komai game da shi, ita ta ƙara ba ni ƙwarin guiwa ma a lokacin. Ashe kawai don ta cutar da ni ne, ita ma waccan ƴar ba jinina ba ce. Ga kuma karayar arziƙi da ta same ni, na rasa komai nawa sai kai da kuma ƙanwarmu Sailubah. Rashin jin daɗin rayuwa ta sa na baro Maiduguri na dawo nan garin Kano wurinka, don na san kai kaɗai ne mutumin da ba zai taɓa gudu na ba. Akwai wani sirri da nake ɓoyo, wanda babu wanda ya san shi sai ni, Safeena da kuma mutum uku da suka taimaka min (Asabe, Rita da kuma ƙanwar Rita). Farouk da kake gani ba shi ne asalin ɗana ba, na same shi ne daga hannun wasu malaman asibiti ta dalilin rasa ƴata da na yi. Riƙonsa kawai nake yi, amma ban haɗa komai da shi ba. Na sani, cewa ban aikata abun kirki ba da na yaudari iyayensa a matsayin ya mutu, wato na ƙuntata musu ni kuma na faranta wa kaina, bayan kuma su za su fi ni jin zafi ma. Tabbas abin da na aikata ne yake bibiyata, ya sa rayuwa ta juye min har izuwa wannan lokacin. Usman ka riƙe shi da amana, don Allah kar ka cutar da Farouk." Kwana biyu da faruwar haka Allah ya karɓi rayuwar Abubakar. Sosai Usman ya yi kuka, ya ƙudiri aniyar riƙon Farouk tamkar ɗan da ya haifa da cikinsa. Ya haɗiye kukansa. Ya ce, "Mu ƴan asalin Kano ne, surutu ya rinƙa dawo min cewa ina riƙon ɗan yaya Abubakar. Gudun kar yaron ya tashi da tunanin ba ni ne mahaifinsa ba, ya sa na nemi transfer daga wurin aiki muka dawo nan garin da zama. Amma duk da hakan labari sai da zo masa har ya gano ba mu ne iyayensa ba. Sai dai bai taɓa tsammanin ba jinina ba ne, a zatonsa ɗan Yaya Abubakar ɗin ne shi kamar yadda na faɗa masa." Cikin kuka Dady ya ce, "Babu shakka Farouk ɗana ne! Ashe ɗana ne Farouk..." Ya saki kuka haɗe da tsinke wayar. Sai yanzu yake tunowa da ranar da Farouk zai rasu. Irin riƙon da suka wa junansu, nutsuwar da suka rinƙa samu. Ashe da rabon zai riƙe ɗan da ya haifa da hannunsa. Da rabon zai ji irin gumin da yara ke ji idan sun riƙe hannun iyayensu. Shi ya sa ya ƙi sakinsa ashe. Da dare Dady ya kira Momy, cikin kuka yake sanar mata yadda abubuwan suka faru. Hankalinta ya tashi sadda ta ji wai ɗanta ne Farouk da ya rasu. Sai ta kuma sakin kuka. Sai da mahaifiyar Ummi ta rinƙa rarrashinta tana ba ta baki. Washe gari Tun da safe suka fara haramar tafiya. Sai dai kuma jirgin sai huɗu na yamma zai tashi. Alhaji Marwan ya kawo shawarar su daure su ƙarisa garin Bama, saboda su Annur su nemi danginsu wanda suke a raye su yi zumunci. A tasha ne aka ba su shawara cewa kar su shiga garin na Bama, har yanzu akwai sauran tashin hankali, kawai dai abun ya yi sauƙi ne. Haƙurar kuwa suka yi. Ƙarfe uku da rabi suka isa Airport, Momy da Yamaira ma drivern gidan su Ummi ya kawo su, bayan an haɗa musu sha-tara ta arziƙi. *** *Na warware muku komai yanzu kam, da alama. Na tabbata cewa akwai wanda ba su taɓa tsammanin cewa Farouk Sardauna ne asalin ɗan su Momy ba. Sai dai na ba ku alama. Ku duba shafi na 53 da kuma na 54, za ku ga alamomin da na bayyana muku, wanda ya kamata a ce tun nan jikinku ya ba ku wani abu. Sai dai ba zan manta ba, Basman Mai sanyinta ta yi wannan hasashen, har ta yi comment a kai. To Habibty Basmah, yau dai kam kin tabbatar da wannan hasashen naki, don haka na ba ki kyautar shafin ma baki ɗaya.* *Gaisuwa zuwa ga Lolita. Na gaishe ki lodi lodi.* *Me ya rage?* *Shafin ƙarshe ko? Za ku ji shi insha Allahu. Na gode ƙwarai da jimirin bibiya ta.* Thanks all. Pinky durling💞 RAZ 2 [9/29, 5:13 PM] Princess Amrah✍🏻💞: *🅰MRAH NAKE SO!♥* _(Labari mai taɓa zuciya, soyayya, sadaukarwa da kuma ban tausayi)_ Sadaukarwa ga masu cutar amosanin jini (Sickler) Na Amrah A Mashi (Princess Amrah) *NAGARTA WRITERS ASSOCIATION* 7⃣5⃣ END Wattpad: PrincessAmrah *** Sadda suka dira cikin gida a lokacin har magrib ta kusa. Maryama da su Hanan dama sun zo sun gyaggyara gidan sannan suka musu girki. Islam ma ta zo sun yi tare da ita. A falo suka zazzauna duka ana miyar da magana. Maryama kuma suna serving ɗinsu abinci. Bayan sun gama jido kayan duka suka zauna. Ta ɗan saci kallon Annur ta ga ita yake kallo, sai ta sakar masa murmushi haɗe da ɗauke kanta. Muryar Sans ta ji ya ce mata, "Maryama sai kika ji wani al'alamarin ubangiji ko. Ashe Farouk Sardauna jinin su Momy ne. Ɗansu ne na cikinsu." Annur ya ce, "Ta san shi ne?" "Sosan sosai ma kuwa. Mallam ai da shi za ta aura sai Allah bai nufa ba. Da yanzu shi ne ba kai ba." Ya ƙarisa maganar cikin zolaya. Bugu Annur ya kai masa. Uncle Marwan ya ce, "Salman ka cika tsokanar faɗa na kula." Duka aka yi dariya har da Dady da Momy. Sai dai su kam ta ciki na ciki, suna jimamin rashin gudan jininsu. Bayan an kira magrib duk suka mimmiƙe. Uncle Marwan ya ce da Yamaira ta tashi su tafi. Maryama ta cicciɓar mata Yesmeen da ke barci. Ta ce, "Ummina da alama ta ji daɗin barcin nan. Tunda kuka shigo take abu ɗaya." Yamaira ta ce, "Ai haka take da barci Yesmeen. Ba ta ko gajiya. School dai za a saka ta idan an koma hutu duk kowa ma ya huta." Bankwana ta ma Momy. Momy ta mata nasiha kan ta ƙara riƙe zumunci, yanzu ba kamar da ba ne. Idan da kawai a matsayin matar alhaji Marwan take to yanzu ba haka ba ne, ta shigo sahun ƴaƴan gidan. Ta ma Momy godiya sosai sannan suka tafi. Bayan Maryama ta dawo har za ta zarce ɗakin su Hanan sai Momy ta kira ta ta dawo. A ƙasa ta zauna kanta sunkuye tana wasa da yatsun hannunta. "Maryama..." Ta ji Momy ta kira sunanta. Da jin haka sai ta tabbatar da cewa magana ce za su yi mai muhimmanci. Ta miƙa dukkanin hankalinta ga Momy. "Maryama a haƙiƙa bani da kalmar da zan yi amfani da ita wurin jinjina miki. Jiya lokacin da Alhaji Marwan yake ba mu labarin gwagwarmayar da kika sha na yi matuƙar mamaki. Ban taɓa tsammanin kyawawan halayen naki har sun kai haka ba. Ashe ƙaramar yarinya kamar ki za ta iya siyar da farin-cikin ta domin nema wa wani bawan Allah lafiya? Na yi mamaki sosai. Yanzu dai nasiha zan daɗa yi miki a matsayina na uwa..." Sallamar Annur da Sans ta ji hakan ya sa ta dakata tana kallon su. Sans ya ce, "Bro fira ake fa tsakanin ƴa da uwa." Annur ya ce, "Ah to ai sai mu zauna a yi da mu." Murmushi Momy ta yi haɗe da ci gaba. "Halin nan naki da na san ki da shi nake son ki ƙara wani a kai. Ki zama mace mai haƙuri, mace mai kamun kai, sannan kuma mace mai adanar sirrin mijinta. Kin ga ciki da kike gani, ba wai don cin abinci kawai aka yi shi ba, har da don ajiyar sirri. Ki guji duk wata ƙawar banza da za ta nemi gusar da farin-cikin mijinki. Ki masa ladabi daidai gwargwadon ikonki. Ki riƙi haƙuri, domin kuwa shi ne baki ɗaya a zaman aure." Ta juya ga Annur. "Kai ma na dawo gare ka. Gwara da Allah ya sa ka shigo ma. Don Allah Annur kar ka zalunci Maryam. Na san ka san yadda ta sha wahala da kai a lokacin da ba ka da wani gata sai Allah. Ta ƙaunace ka da zuciya ɗaya a irin lokutan da ba lallai ba ne ba ka samu masoyi. Ta bijirewa zaɓin iyayenta duk don ta faranta maka. Ina son ka ƙoƙarta saka mata da kyautatawa, kamar yadda Allah maɗaukakin sarki ya ce sakamakon kyautatawa yana ga kyautatawa. Ka fitar da haƙƙin iyalinka. Ka guji duk wata zugar abokan banza, babban burinsu shi ne su ga sun raba kanku. Ina so ka zama ita ta zama kai. Ko mu nan ba na fatar ranar da za ka kawo min ƙarar Maryama cewa ta yi maka wani abu. Idan ma ta maka ɗin, to don Allah ku daure ku sasanta kanku a tsakaninku. Ka yi haƙuri da ita, duk wuya duk runtsi kar ka butulce mata." Kanshi a ƙasa yana jin daɗin nasihar ta Momy ya ce, "To insha Allahu Momy. Mun gode ƙwarai." "Saura kuma nan da shekara ɗaya mu ji ka ce za ka ƙara aure, don ba za mu lamunci wannan ba." Dungurar masa kai Momy ta yi tana murmushi. "Allah kuwa Salman sai na ci maka. Kuma ko ka fitar da mata kai ma ko in je cikin matan nan masu kawo tallar fura a wancan sabon ginin da ake yi na nema maka auren ɗaya." Dariya suka saka su duka. Dady da ke daidai shigowa ɗakin ya ce, "Ai dai ya ga ga ɗan uwansa nan ya zama magidanci. Shi kuwa ya yita zama a haka." Maryama cikin zolaya ta ce, "Dady ai ya tsayar da mata fa. Ni kaɗai ya faɗa wa ita." "Ah to faɗa min sarakuwar in ji ta mana ƴata Maryama." "Dady kar ka damu. Ai tsakaninmu ne, kar kuma ya ce ba zai sake faɗa min sirrinsa ba." Momy ta taɓe baki haɗe da yin murmushi. "In ta yi tsami ma ji ai." Hararar Maryama ya yi Sans. "Ni da yaushe na yi da ke wai na tsayar da mata?" Ta ɗora hannunta a ka kamar da gaske. Ta ce, "Ji min mutum zai nuna bai san an yi ba. Kai dai kawai ka yi ladabi ko kuma na fallasa sirrin." Islam ta fito hannunta riƙe da na Abdul da ke neman faɗuwa saboda barcin da ya yi. Da sauri Maryama ta je ta riƙo shi. "Haba mana Aunty Islam. Ji fa yadda kike jan shi kamar ba mutum ba." "Yo Maryama idan ba jan nasa ba ya zan yi da shi. Wannan gardin dai ai ba iya ɗaukarsa zan yi ba." "Ni zan iya." Maryama ta faɗa. Ta kuwa ɗauke shin sannan Islam ta ma su Momy bankwana. Momy ta ce, "Mun yi waya da Saddiqa ai. Ita ke faɗa min wai kun yi waya kin ba ta labarin komai. Ta dame ni da kuka nikam na kashe wayar. Za ta zo jibi ma wai." Islam ta ce, "Ehh haka ta faɗa min. Ta damu ne sosai ni ma kukan take ta yi min, har na ji dama ban faɗa mata ba tun farko. Wai za ta zo har gidan su Amrah mu je mu ba ma Ummanta haƙuri abubuwan da suka faru a baya." Sai Annur ya ji faɗuwar gaba. A duk sadda zai ji an ambaci sunan nan to sai gabanshi ya faɗi. Hakan bai rasa nasaba da zaman dirshan ɗin da ta yi a cikin zuciyarsa, wanda fitarsa ba abu ne mai sauƙi ba. Maryama na dawowa daga rakiya Momy ta ce ta tashi su tafi dare na yi. Dady ya ce da Annur next week zai koma aiki a matsayinsa na architecture na companynsu. Shi kuma Sans ya ci gaba da zama a matsayin CEO baki ɗaya. A cikin mota Annur ya kamo hannun Maryama. Ya kalle ta sannan ya miyar da kallon sa ga tuƙi. "Na yi kewarki sosai." Ta harare shi. "Ban taɓa gani ba sai yau." "Me?" Ta faɗa cikin mamaki. "Yo da Hausawa ke cewa wai aikin banza harara cikin duhu. Ban gasgata ana yin ta ba sai yanzu a wurin matata." Ta taɓe baki. "Ashe dai ba a duhun ba ne tunda dai har ka san na harare ka ɗin." "To na ji. Yanzu dai faɗa min wace mata ce kika ce kin wa Salman? Don kar sai mun je gida ki ce ki faɗa min, bayan kuma kin san ba lokacin irin wannan hirar ba ne." "Mutumin nan kai ko." "Ni me? Gaskiyata fa na faɗa malama." "To na ji. Hadizar nan ka tuna ta?" "Wace ma?" Ya tambaye ta. "Wacce na faɗa maka ita ta yi silar da har muka san cewa kana Maraɗi. Budurwar Yah Salman ɗin ce dama. To ita na zaɓa masa a matsayin mata. Na tabbata ba za ta ƙi shi ba, kamar yadda shi ma ɗin ba zai ƙi ta ba. Na yi waya da ita ma ta ce ta amince. Ina so ne mu ƙulla zumunci da ita har ƙarshen rayuwarmu. Saboda gudummuwa da ta bayar na samuwar ka." Ya jinjina kansa haɗe da riƙo hannunta. "Kina da brain sosai Baby. Tabbas tunanin nan naki ya yi sosai." "Dama ina so mu je Maraɗin, an ce Fiddou ta yi aure. Ina so mu je mata kana cikin hankalinka, ka mata godiya na ɗawainiya da kai da ta yi, da kuma soyayya da ta gwada maka a lokacin da ka yi rashin gata." Yana murzar hannunta ya ce, "Ni ma kaina na yi tunanin hakan. Amma me ya kamata mu kai mata?" "Ina da manyan frames a ƙarƙashin gadona, dayake nawan sun so su yi yawa, Mama ta siya kuma sai ga gifts da akaita samu na frames ɗin. Sai a ɗauki ko guda uku a tafin mata da su." Annur ya ce, "To masha Allahu. Hakan za a yi. Ɗazu a mota bayan an ɗauko mu daga Airport Uncle Marwan ke ce min wai dole sai na miki lefe. Saboda ba wani abun kirki ne a cikin wanda ya yi ɗin ba. To Momy dai ta ce in bari ba sai na yi ba, za su yi komai a kawo miki. Ni dai na ga cancantar na yi miki ɗin, zan kuma yi insha Allahu sai ki haɗa duka. Dady kuma ya ce zai yi ƙoƙari a ci gaba da wannan ginin na jikin namu, part biyu ne a cikinsa, amma da ƴar tazara a tsakaninsu, sai mu zauna ni da Salman idan ya yi aure." Cikin jin daɗi ta ce, "Allah ya tabbatar mana da alkhairi Yaya. Allah kuma ya bar mu tare har ƙarshen rayuurarmu. Allah ya kawo ranar da zan haifa mana little Amrah." "Amin." Ya faɗa a daidai isowarsu bakin gate. Horn ya yi mai gadi ya buɗe musu gate ɗin suka shige. Dama sun yi sallolinsu. Kai tsaye bedroom kawai suka wuce saƙale da juna. "Yaya ka samu ka watsa ruwa. Ni ma zan je ɗakina na watsa ko zan ji daɗi a jikin." "Ki je ina?" Ya ƙwalalo ido yana kallon ta. "Dakina mana." Ta ba shi amsa haɗe da tunzuro baki. "Ai malama ki ɗauka cewa wanan ɗakin naki ya zama ɗakin baƙi. Kayanki ma duk kwaso su za ki yi ki dawo da su nan. Shara kawai za ta rinƙa kai ki can. Bari ma ki ga." Ya kama hannunta suka nufi toilet ɗin. Sai ta tuno ranar farko da ta fara yi masa wanka. Ta runtse idonta tana sakin murmushi. Bayan sun gama suka fito a cikin towel ɗaya. Mai suka shafa sannan suka miƙe a tare ta fitar masa da rigar barci. Sai da ta saka sannan ta ce da shi za ta je ɗakinta ta ɗauko kayan barcin ita ma. Doguwar riga ce ta sako wacce iyakacinta bisa guiwa. Yadinta santsi gare shi irin mai kwnaciya a jikin nan. Ga wata irin humra da ta shafa wacce Islam ta kai mata yau. Sai duk ko'ina ya game da ƙamshin humrar. Ta same shi ya zauna bisa stool ya dumtse hannunsa na dama. Murmushi ta saki bayan ta iso gare shi. Ya kama hannunta na hagu. Yatsar kusa da ƴar ƙarama ya kama, ya buɗe hannun nasa ashe zoben nan ne a ciki. Ta bi shi da ido har ya zura mata zoben. "Haƙƙin Amrah ne, amma mahaifiyarta ta ba ni kyautarsa. To ni ma na ba ki kyautarshi da zuciya ɗaya. Ina so ki ɗauka cewa ke kaɗai ce a zuciyata idan har aka cire Amrah da ta daɗe a ciki tun ina yaro. To ki saka a ranki ƙaunar da nake yi ma Amrah ba komai ba ce a yanzu, tunda dai ta tafi babu ita. Ke ɗin dai ce, zan kuma ci gaba da ƙaunar ki har ƙarshen rayuwata." Tsabar jin daɗi ba ta san sadda ta rungomo shi ba tsam-tsam a jikinta. Numfashi take saki, tana jin yadda ƙaunarsa ke ƙara shiga cikin zuciyarta. A nashi ɓangaren ma haka ne. Daga nan sai suka faɗa duniyar soyayya. A gida kuwa tun bayan tahowar su Annur Momy ta shige ɗaki tana kuka sosai. Tana jin yadda soyayyar ɗanta da ya rasu ke daɗa wanzuwa a cikin zuciyarta. Dady ke ta rarrasarta yana ba ta baki har ya samu ta yi shiru. Washe gari Misalin sha ɗaya na safe Maryama na kitchen ita da Annur suka ji knocking. "Mallam ka ƙyale ni in dubo mai knocking please, ka wani ƙanƙame ni duk ka hana ni saƙat wallahi." Annur ya ce, "Su ma dai baƙin, su rasa lokacin zuwa sai irin wannan da nake jin daɗin kasancewa manne da ke?" Ta gyaɗa kanta. "Please mana yah Noor. Babu fa daɗi mutum yaita tsayuwa ba a buɗe masa ba." "Aunty masifa na ji to. Je ki, amma ki yafa mayafi." Ba ta ko tsaya saurarar sa ba ta doshi falo. Sai da ta fara saka hijabinta sannan ta isa ta tambaya waye. Muryar mace ta ji ta ce, "Maƙoftanku ne da suka dawo shekaranjiya." Da sauri Maryama ta buɗe ƙofar. Kyakkyawar mace ta gani tsaye da mijinta, sai kuma wasu yara guda biyu babba da ƙarama. Murmushi ta sakar musu haɗe da ba su izinin shigowa har da mijin. "Sannunku da zuwa. Last week fa na ji ana ta kawo kaya, ashe ku ne kuka dawo gidan." Matar cikin sakin fuska ta ce, "Wallahi kuwa mu ne. Yau kwananmu biyu da dawowa ai." "Ah to masha Allah. Ƴan yara sannunku." Ta kama hannun babbar. "Good morning Mama." Yarinyar ta faɗa cikin ladabi har da rusunawa. "Morning my dear. Ina zuwa." Ta miƙe. Kitchen ta nufa ta same shi. Ta ɗika masa duka. "Mallam ai sai ka fito mun yi baƙi. Sabbin maƙwaftanmu ne har da mijin duk na ce su shigo." "Ok to bari in je." Ya fita. Ita kuwa lemuka ta jera a tray ta fita da su. Hannu ya ba namijin suka gaisa. Sannan matar da yaran duk suka gaishe shi. "Ga lemu nan ku sha." Maryama ta faɗa tana murmushi. Matar ta ce, "Wallahi mun gode. Ai dayake safiya ce, karyawarmu kenan." Mijin ne ya yi magana cikin sakin fuska. "Ni sunana Khalid, matata kuma Ikram (Wanda ya karanta littafin SHI NE SILAH zai san su) waƴannan kuma yaranmu ne, Feenah da Ummu Ruman. Ina so mu ƙulla zumunci, tare da riƙe amanar juna." Annur ya murmusa. "Insha Allahu kuwa. Daga yanzu ka zama abokina Khalid. Ikram ma kuma ta zama ƙawar Maryama. Zumunci ya ƙullu kenan har abada." "To masha Allahu." Khalid ɗin ya faɗa. Sun ɗan jima suna taɓa fira kafin Khalid ya ce su tashi su tafi rana ta yi. Sosai Maryama da Annur suka nuna jin daɗinsu, sannan suka yi musu alƙawarin za su shigo su ma da izinin Allah. Washe gari Bayan sun gama karyawa Annur ya ce da Maryama ta shirya yau su tafi Maraɗi. Saboda ya fi son a yi komai kan lokaci, duk da dai cewa Hadizar ta ce da Maryama ta amince amma dai ya kamata su yi maganar face-to-face. Tana cikin shiri Jiddah ta kira ta cewa ga ta nan ta zo tana knocking a buɗe mata. Da farin-ciki Maryama ta je ta buɗe mata ƙofar. Zama suka yi fara'a ƙunshe a fuskokinsu suka gaisa. Ledar hannunta ta miƙa wa Maryama cewa kayan saka ranar su ne ita da Deedah. Tun shekaranjiya Abba da Kawu Imrana suka kai kayan. Maryama ta kumburo fuska. "Yanzu don Allah sai a kai kayan saka rana amma a rasa wanda zai faɗa min? Ko da safen nan fa sai da na yi waya da Abba da Mama. Dama na ji Hammad na neman faɗa min wani abu kuɗin wayar tawa suka ƙare kuma bai kira ba. Ashe ƙawata amarcewa za a yi. Yaushe ne auren?" Jiddah ta ce, "Wata ƙila zance ne bai kawo ba. Yanzu dai ai ga shi nan kin ji daga gare ni." "Na ji kam. Yaushe za a yi ba ki faɗa min ba." "Wata biyu ne aka saka." "To Allah ya nuna mana." "Amin ya Allah. Ina Yah Noor da jiki?" Maryama ta yi murmushi. "Yah Noor kam alhmdulillah. Bari in kawo miki shi ku gaisa." Ta tafi ɗakinsa. Labari ta ba shi sannan ta kamo hannunshi suka dawo falon. Tana ganin shi sai ta ga duk ya mata ƙwarjini, saboda duk wannan yaƙen da yake yi a baya babu shi yanzu. Ga kyau da ya yi sosai kamar ba shi ba. Ta gaishe shi. A maimakon ya sakar mata dariya kamar yadda ya saba yi idan an gaishe shi sai ta ga akasin haka. "Lafiya lau Jiddah. An zo lafiya ya su Mama?" Cikin mamaki ta ba shi amsa da lafiya lau. Maryama kanta ta san cewa Jiddah mamaki ne ya cika ta. Annur ya kalle ta da murmushi. "Baby your friend is suprised. Zan shiga ɗaki, explain everything to her." Ya ba ta peck a hannu, sannan ya nufi ɗakinsa. Jiddah ta bi shi da kallo har ya shige ɗaki. Maryama ta dawo kan kujerar da Jiddah take, ta zauna bisa hannun kujera. Nan ta labarta wa Jiddah duk yadda abubuwan suka faru. Sai ta riƙe baki cike da mamaki. "Maryam kina nufin duk zaman nan wai Yah Noor ya warke kallon mu yake kyar?" Kai Maryama ta ɗaga mata. "Ba ma wannan ne abun mamakin ba. Wai Farouk Sardauna dai da na sani shi ne ainahin ɗan su Momy? Dama dai gaskiya akwai alamar tambaya. A ce tsakanin Sans da Annur babu wani bambanci kamar su ɗaya. Ba zai yiu a ce coincident kawai ba ne. Dole sai identical twince ne za su yi irin wannan kamar." "Haka ne kam. Kin dai ji yadda Allah ke tsara al'amarinSa." Miƙewa Jiddah ta yi. "Ni zan tafi Maryam, akwai wuraren da zan je idan na koma gida." "Ke don Allah Jiddah tun yanzu?" Jiddah ta ce, "Zan dawo ai kar ki damu. Amma fa ina son jin kyakkyawan labari in the next two weeks." Harararta Maryama ta yi, ta raka ta har bakin ƙofa, ta shaida mata cewa Maraɗi ma za su tafi yanzu. "Aikuwa kun kyauta sosai wallahi. Please ki gaishe min da Fiddou, ki ce ina mata fatar alkhairi. Hadiza kuma idan komai ya tabbata insha Allahu da mu za a yi biki." "To zan faɗa musu insha Allahu. Ki gaishe da su Mami." * Misalin ƙarfe biyu da rabi suna cikin garin Maraɗi. Hadiza ta faɗa musu inda za su yi mahaɗa, suka ɗauke ta. Kai tsaye gidan Fiddou suka fara zuwa. Bayan Annur ya faka motar a ƙofar gida Hadiza ta fita da frames da Maryama ta ce mata ta ɗauka a bayan motar. Kafin Maryama ta fita ya ce "Ki gaishe ta. Idan kuma mijinta ya bada izini sai in shigo har ciki na musu godiyar da kaina." Maryama ta ce masa to, sannan ta ɗauki hand bag ɗinta ta fice. A falo suka same ta kwance ƙasa, Mahmouda na yi mata fifita. Sallama suka yi, ya amsa haɗe da ɗago kai ya kalle su. Bayan sun shigo ciki suka zauna, da sakin fuska ya amsa gaisuwar da ya musu, kasantuwar bai san Maryama ba, Hadiza kawai ya sani. "Barci ma take yi ko?" "Walle kam ba ta da lahiya ne. Daga asibiti ma muke." Hadiza ta yi dariya ta ce, "Hala dai ta kamu ne." Dariyar shi ma ya yi, "Ba ki gajiya Hadiza." "Aikam tashin ta za ka yi. Baƙi ne ta yi tun daga Katsina. Maryama da kuma mai gidanta Annur yana waje cikin mota shi ya kawo mu." Ba zai taɓa manta duka sunayen biyu ba. Saboda har gobe suna da daraja sosai a zuciya da kuma bakin Fiddou. Sau da dama takan ambaci sunayen a duk sadda wani abu zai faru mai kama da nasu. Sai ya saki murmushi. "Ahh sannunku da zuwa. Halan mi da bai shigo ciki ba? Bari in tai in shigo da shi. Fiddou!" Ya bubbuga ta ta tashi. Murtsukar idanuwa ta fara yi. "Sahibi mi kuma?" Murmushi ya sakar mata. "Baƙi kika yi." Ta tashi zaune shi kuma ya nufi waje domin kiran Annur. Tana haɗa ido da Maryama ta ƙarisa murmurewa. Ta saki baki da ido tana kallon ta. "Wata nake gani kamar dai Maryama." "Ni ce fa da kaina mai ciki." Harara Fiddou ta kai mata. "Babu ko gaisuwa sai tsokana ko?" Hadiza ta ce "Babu wani tsokana sai gaskiya. Malama ki ga yadda kika koma, ko mutum bai san mai ciki ba ya gan ki sai ya gane. Mu dai Allah ya raba lafiya mu samu ɗa ko ƴa." A daidai nan Mahmouda ya shigo riƙe da hannun Annur suna dariya. Fiddou na haɗa ido da shi sai da ta yi mamaki. Ba ta bar maganar a zuciyarta ba sai da ta tambayi Maryama. "Halan dai Modu ya warke Maryam?" Maryama ta ɗaga mata kai tana murmushi. "Ya warke Fiddou. Hadiza ba ta faɗa miki aurena da shi ba?" Ta gyaɗa kai. "Ta dai hwaɗi min ana aurenki rana guda da nawa. Amma ba ta hwaɗi min Annur za ki aure ba." Maryama ta ce, "Aikuwa shi na aura Fiddou. Ga shi nan kuma ya warke garas kamar bai taɓa yin wani ciwo ba. Abin da ya sa muka zo dama godiya za mu sake yi miki, shi ma kuma ya miki da kansa." Annur ya yi murmushi, ya ce, "Haka ne. Malama Fiddou ya gida ya ƙarfin jiki? Mallam Mahmoud ya ce min daga asibiti kuke." Cikin kunya ta ce, "Alhamdulillahi." "To masha Allah! Duk da dai ban san ta inda zan fara ba, addua ce kawai daidai da ke. Allah ya saka miki da alkhairi Fiddou. Kamar yadda kika taimake ni ke ma Allah ya taimaka miki har ƙarshen rayuwarki. Allah ya dauwamar da farin-ciki a rayuwar aurenku. Allah ya ba ku zuria mai albarka." Mahmouda ya amsa da, "Amin. Ai babu komai Annur." Ruwa ta kawo musu suka sha sannan suka miƙe cewa za su tafi gidan su Hadiza. Bankwana suka musu sannan suka kama hanyar gidan na su Hadiza. Tare suka fita daga motar, Hadiza na gaba suna biye da ita har suka shiga cikin gidan. Yayanta suka nemi ganawa da shi. Bayan sun gaisa Annur ya masa bayanin abin da ke tafe da su. Karara ya nuna jin daɗinsa. Saboda yawon ta-zubar ɗin da Hadizar ta yi a baya, amma cikin ikon Allah dama ta nadama ta dawo har ta yi istibra'i, mijin auren ake nema. Don haka duk sadda suka shirya kawai su zo a ɗaura aure, babu buƙatar ɓata lokaci tunda dai ba aure ba ne za a yi kamar irin na ƴan mata. Annur ya ji daɗi sosai, ya ce insha Allahu iyayensu za su zo bai ɗaya a ɗaura auren a tafi da amarya. Godiya suka masa sosai sannan suka miƙe. Hadizar ta raka su har mota ita da yayanta, suka tafi suna jinjina halin karamci irin na mutanen. * Doya da ƙwai take soyawa, amma ji take zuciyarta na tashi, kamar ba ta son warin ta. Famar doɗe hanci ta kama yi, amma sai tsananta abin ke yi. Annur da ke daidai shigowa kitchen ɗin ya ce, "Baby lafiyarki kike famar doɗar hanci?" Ba ta buɗe hancin ba ta ce, "Wallahi ƙamshin doyar ne ba na so." "To fa! Ko zazzaɓin ne har yanzu?" "Na ji sauƙin zazzaɓin Baby. Da shirin tafiya lecture ma nake yi wai nan. Tashin zuciya ce kawai nake ji, kuma ƙamshin ne da ba na so..." Tun ba ta rufe baki ba ta ji amai ya taso mata. Da gudu ta isa wurin sink ta hau kwara amai. Ba wani abun kirki ba ne ba a cikin dama. Guntun doughnut ne da yoghurt da ta yi sammakon sha, saboda yunwar da ta tashi da ita. Da hanzari ya isa gare ta yana mata sannu. Take daga yin amai duk sai ta galabaita. Ya kamota ya riƙo bisa jikinsa. Yana ƙara ce mata sannu wani aman na zuwa, a jikinsa ta ci gaba da kwara shi. Bai ji ƙyama ba ko kaɗan, sai ma tausaya mata da ya yi sosai, ya hau yi mata sannu. Ƙauri ya ji alamar doyar ta soye har man ma ya gama yin baƙi. Ga kuma Maryama a jikinsa. Da sauri ya ɗauke ta ɗaf, ɗayan hannunsa ya sa ya kashe gas ɗin sannan ya nufi toilet ɗin ɗakinsa da ita. Rigar jikinta ya cire mata, ya wawwanke mata baki da wuyanta sosai da sabulu sannan ya ɗauro mata towel ya kwantar da ita bisa gadon sa. Banda sannu babu abin da yake mata. Tausayinta yake yi sosai, yana ji kamar ciwon ya dawo a jikinsa. Kayan nata ya ɗauka ya fita da su can corridor ya jefa a washing machine ya wanke sannan ya cire rigarsa ma ya wanke. Dawowa ya yi ya fiddo mata rigarsa long sleeve ya saka mata. Sannan ya ɗauko wani skirt nata na English wears ya saka mata yana yi yana ce mata sannu. Jin wayarsa ya yi tana ƙara. Da sauri ya duba mai kiran ya ga Salman ne. "Ango lafiya dai ko?" Ya faɗa cikin muryar gajiya. "Lafiya ƙalau Annur. Wani aiki ne ya taso a Office yanzun nan Mu'azzam ya kira ni. Ya ce min kuma kai ma ba ka je ba." Annur ya ce, "Wallahi na yi shirin tahowa to kuma Maryam jikin babu daɗi. Asibiti ma zan kai ta yanzu. "Subhanallahi! Me ya same ta?" "Zazzaɓi ne dai take ta fama da shi kusan five days back, to yanzu dai abun ya yi worst, ba ta da wani ƙarfi sosai." "Ya salaam! Gaskiya ka gaggauta kai ta asibiti. Bari in kira Mu'azzan ɗin a tsayar da aikin har zuwa gobe idan Allah ya kai mu. Allah ya kyauta ya ba ta lafiya." "Ameen Salman. Ka gaishe da Hadizar." "Za ta ji." Ya faɗa haɗe da tsinke wayar. Mukullin motarsa ya ɗauka ya je ya buɗe ta ya sa mai gadi ya buɗe masa gate, sannan ya koma ya cicciɓo ta. Wayarsa da tata ya ɗauko sannan ya datse ƙofar bayan ya kwantar da ita a kujerar gaba. K-Dara Specialist Clinic suka nufa. Sai da aka fara buɗe mata kati sannan aka tura ta layin ganin likita. Har a lokacin tana kwance a jikinsa, sannu yake ta yi mata. Ana zuwa kansu ya kama ta suka shiga. Likitan ya nemi sanin abin da ke damun ta Annur ya masa bayani. Takarda ya basu cewa a je a yo awon fitsari da na jini. Ganin yadda jikin nata ya galabaita sosai ya sa ya ce dole za a ba ta gado a saka mata drip don walwalarta ta saitu. Nurses ya kira suka kai ta ɗaki, amenity aka kama mata Annur ya biya, aka yi mata duk gwaje-gwajen da suka kamata. Sai a sannan ya kira gida ya sanar wa Momy, sannan ya kira gidan su Maryama ma ya faɗa ma Mama. Yana gama waya da Mama Salman ya kira ya ji ya jikin? Ya ce da shi ma an kwantar da ita. Fatar samun sauƙi ya mata sannan ya ce anjima za su zo da amaryarsa Hadiza. Bayan duk results sun kammalu likitan ya nemi ganinshi. A nan ya masa albishir da cewa Maryama na ɗauke da juna biyu na wata guda da sati ɗaya. Hamdala ya yi ga Allah cike da farin-ciki ya baro Office ɗin. A hanya ya ci karo da Dady da Momy sun zo duk a ruɗe. Ganin sa da suka yi yana murmushi duk sai suka yi turus suna kallon shi. Momy ta ce, "Ta ji sauƙi kenan ma." "Ehh alhmdulillah! Mu je na kai ku ɗakin." Suka bi bayanshi har zuwa amenity room 4. A kwance suka same ta an rufe ta da blanket da ya aro a ɗaki na kusa da na Maryama. Cikin ruɗewa Momy ta tattaɓa jikin Maryama da aka liƙa wa drip tana barcin wahala. "Allah sarki! Sannu Maryama. Me yake damun ta ne Annur?" Sosa ƙeyarsa ya yi haɗe da sakin murmushi. Bin shi da kallo suka yi. Dady ya yi murmushin shi ma. "Ah to da alama dai jika muka samu. To Allah ya raba lafiya." Sai ma yanzu ta ƙara kallon Maryama sosai ta ga fayau ɗin da ta yi. Ta kamo hannunta ta riƙe. "Ashe dai jika ne ke wahalar min da ƴa. To Allah ya sauƙaƙa ya rangwanta miki." Ta ƙarisa rufe ta da blanket ɗin. Ya sosa kansa ya ce, "Momy to tunda kun zo bara in samu komawa gida in harhaɗo abubuwa. Ko bargon nan aro shi na yi wancan ɗakin." Momy ta ce, "To shi kenan. Sai ka ɗauko kafet ɗin sallah ma. Daga nan ka biyo da flask na ruwan zafi da kayan tea. Ga shi ko girki ban ƙarisa ba na baro gidan." Dady ya ce, "Kin dai kashe ko?" "Na kashe." Ta ba shi amsa. "Ok to da kyau. Mun yi waya da Nadrah ai ta ce wai Hanan da Janan dai sun ce nan za su dawo baki ɗaya. Da suka koma ɗin nan duk sai suka ji daban. Kuma babansu ya bar su." Annur ya ce, "Ah to masha Allahu. Ni fa dama har zan ce ya kamata Momy ta samu mai aiki haka nan. Wai ina ma asalin waccan ɗin?" Momy ta yi murmushi. "Salman ya korar min da kaf masu aiki." "Bari in je to Momy." Ya tafi. Da dare ɗakin ya cika da ƴan dubiya. Salman ma ya ɗauko amaryarsa Hadiza da kwanansu huɗu da aure yau. Baba da Mama ma sun zo tare da Hammad. Momy dama ba ta tafi ba tana nan. Sai ga Islam da mai gidanta sun zo Abdul-Ahad biye da su. Jiddah ma ba a bar ta a baya ba. Deedah ya kawo ta, saura sati biyu bikinsu. Suna nan sai ga Uncle Marwan ma da Yamaira wacce ƙaramin ciki ya fara bayyana a jikinta. Kwananta biyu a asibitin aka sallame ta tare da ba su shawarwarin yadda za su kula da cikin sosai. Sannan kuma aka faɗa mata sadda za ta fara zuwa awo. A mota shagwaɓa kawai Maryama ke sakar masa. Abu kaɗan ta kama ƙuhin kuka. Shi kuwa sai famar rarrasar ta yake yi har suka isa gida. Cikin kwanaki biyu Maryama ta fara samun sauƙi. Annur abu kadan ya tambaye ta me ya faru? Me take so? Idan ma wurin aiki ya je to suna tare a waya, saboda ba ta koma School ba Dr. Ya ce ta bari har ta ƙara warwarewa. Duk hidindimun bikin Jiddah babu wanda aka bar Maryama da Annur a baya. Tare suka rinƙa zuwa events ɗin ciki kuwa har da dinner. Ranar ɗaurin aure aka shafa fatiha, Jiddah ta zama amaryar Deedah, kowa ya shaida hakan. Da yamma aka ɗauki amarya aka kai ta tafkeken gidanta da ke Batagarawa lowcost, kasantuwar Deedah ya samu lecturing a jamiar Umaru Musa nan cikin garin Katsina. Har da Maryama aka saka ango ɗaki. Ta ma amarya nasiha sosai ta mata gyare-gyaren gida, misalin goma da rabi Annur ya zo ya ɗauke ta. Haka suka ci gaba da rainon cikinta kuma tana zuwa makaranta abin ta. Ranar wata laraba da yamma naƙuda ta kama Maryama. Dama Hanan da Janan sun dawo, Hanan aka kawo mata tana kwana tare da ita. Janan kuma tana gida tare da Momy. Annur ba ya gida a lokacin. A ruɗe Hanan ta ɗauki wayarta ta kira Annur ta sanar da shi halin da ake ciki. Cikin kiɗima ya ce da ita yana hanya dama. Ta harhaɗa komai kafin ya iso. Baby wardrobe ta buɗe a ɗakin Maryama ta fiddo kaya uni-sex guda huɗu da overrole guda biyu, tunda dama duk an faɗa musu twince ne a cikin Maryama. A kit ta haɗo da diaper da duk wani abu da za a nema. Tana gamawa Annur na isowa. Yadda ya ga halin da Maryama take ciki duk sai ya daɗa tausaya mata. Kamar ya mata kuka ya ji, ya kinkime ta ya kai mota, Hanan ma ta shiga motar suka kama hanyar asibiti. Sai da suka isa sannan Hanan ta kira Momy ta sanar mata. Annur kuma ya kira gidan su Maryama ya faɗa. Bayan an shiga labour room da ita su Momy suka iso. Mama ma suka iso a ruɗe suka haɗe da su Momy. Dukkansu bakin labour room ɗin suka tsaitsaya suna jiran tsammani. Annur kam tagumi ya yi da dukka hannuwansa, har hawaye na zirara daga idonshi. Ta jima tana naƙuda, kusan awa huɗu tana abu ɗaya har duhu ya fara, sannan ta haifi namiji. A take kuma ta kama wata sabuwar naƙudar. A nan ba ta wani sha wahala sosai ba sai ga ƴa mace ta haifa. Hamdala ta saki bayan fitowar yarinyar. Da sauri ɗaya daga cikin nurses ɗin ta fita waje. momy da Mama har rige-rigen tambayarta suke. "Congratulations! Ta haifi twince mace da namiji yanzu za a kimtsa su duka har da uwar. Tana cikin lafiya ita da yaranta." Annur daga nesa ya ji maganar, aikam sajdatushhukri ya yi, yana jin farin-ciki lulluɓe da zuciyarsa. Isowar Salman da Hadiza kenan su ma suna ji suka yi hamdala ga Allah. Take suka yita kiran ƴan uwa da abokan arziƙi ana sanar da su haihuwar. A nan suka kwana, Hanan da Mama suka kwana tare da Maryama. Mama sai fama take da ita a kan ta shayar da yaran amma turo bakinta kawai take yi wai zafi. Haka dai suka yita fama har gari ya waye. Annur ya zo da kayan kalaci da ya karɓo daga wurin Momy. Suna cikin karyawa ma aka ba su sallama. Bayan sun gama duka suka rankaya suka koma gidansu da suka koma watanni biyar da suka gabata. A cikin kwanakin nan shida kafin suna kullum gidan cike yake da ƴan barka. Babu wanda ba ya yaba kyawun yaran. Ga su dai jarirai amma hakan bai hana kyawunsu bayyana ba. Jidda da ta zo da ƙaramin cikinta sai famar kallon yaran take yi, ba ta ma so a karɓe su. Daren suna da dare Annur ya nemi ganawa da Maryama a part ɗinsa. Bayan ta zo ya ce, "Uwar biyu dai." Ta sakar masa murmushi. "Kai kuma uban biyu." Ya shafi fuskarta. "Na ji dai. Dama ce miki zan yi an siyo komai da kika rubuta. Maganar sunan yaran, nake neman shawararki." "Ban gane ba." "Ina nufin wai sunan da za a saka musu. Miye raayinki? Tun ranar da aka haife su na so na musu huɗuba, to kuma su dama can da sunayensu, Hassan da Usaina, amma dai daga bayan nan na ji shaawar mu musu suna kawai." Ta sakar masa murmushi. "Macen dai na yi mata suna." "Namijin fa?" "Na bar maka zaɓi." Ta ba shi amsa hannunsa riƙe da nata. "To wane suna kika yi mata?" Kallon cikin ƙwayar idonsa ta yi, ta ce, "Amrah..." Tun ba ta rufe baki ba ya jawo ta a jikinsa cike da farin-ciki. "Sosai raayinmu ke tafiya a tare Maryama. Haka nake fatar ɗorewarmu, komai namu ya ci gaba da tafiya tare, soyayyarmu ta ci gaba da bunƙasa. Allah kuma ya raya mana yaranmu." Ta janye jikinta daga nasa. "Dady kar kuma a wuce gona da iri. Jego dai nake yi." "Ba za a wuce ba uwar biyu. Ba ki tambaye ni sunan da na zaɓa wa namijin ba" "Sai ka faɗa Dady." Ya ɗan lumshe idanuwansa. "Farouk na zaɓa masa. Na tabbata su Momy za su ji daɗi sosai. Kuma hakan ne kawai zan yi na kwatanta kyautatawarsu a gare mu. Allah dai ya sa ya miki." "Ko bai min ba ya min Dady, bare ma kuma ya yi ɗin. Allah ya raya mana little Farouk da little Amrah. Allah ya albarkaci rayuwarsu." "Amin ya Rabb. Sai ki tafi ko kar a neme ki." Ta miƙe ta masa bankwana sannan ta tafi. Haka sunan ya kasance cike da farin-ciki. An ci an sha, an kuma yi nishaɗi. Fiddou da Mahmouda ma ba a bar su a baya ba sai da suka zo. Aunty Saddiqa ma ta zo da yaranta. Aunty Nadrah ce kawai ba ta samu zuwa ba daga Cyprus. Yamairah ma ta zo da jinjirinta mai suna Kamal. Sunan ya tara mutane sosai. Kowa ya saka ma Farouk da Amrah albarka. Sai dare sannan aka warwatse. * Gyaɗa kanta ta yi cike da takaici, ta ce, "Wai Farouk me ya sa kake da jan faɗa ne? Tun ɗazu Saddam ke kawo min ƙararka sai ka ce sharri yake yi maka. Kuma dai ga shi Amrah ta tabbatar min da kai ne ke tsokanar tasa. Ba ka jin kunya ƙaninka fa ne kuma saboda kai ya zo hutu gidan nan. Haba Farouk!" Kunnuwansa ya kama tun kafin ya matso inda take. "Am sorry Ammi. Ba zan ƙara ba." Ta masa murmushi. "Yauwa yarona. Allah ya maka albarka ka ji. Zo ka ɗaukar min Baby Hoodah in shiga toilet in dawo." Yarinyar ƴar kimanin watanni biyar ya ɗauka. Kusan faɗuwa suka yi Maryama ta ce, "Farouk bi min ƴa a hankali ni dai." "To Ammi." Ya faɗa bayan sun fita daga ɗakin. Amrah ta yi zaune wuri guda tana duba wani littafi a hannunta. Muryar Saddam ta ji ya ce, "Yaya Amrah me kike yi?" Ta sakar masa murmushi. "Saddam ina duba karatun da aka mana ne a islamiyya jiya, huruf ne. Idan na gama gwanancewa anjima sai in koya wa Farouk." Saddam ya ce, "Kin ji daɗinki ke kam Yaya Amrah." "Kai ma za ka ji ai, musamman ma dai idan ka dage ka yi karatu sosai. Dady da Ammi sun sha ba mu labarin Amrah, asalin wacce aka saka min sunanta. Mace ce da ta zama abar alfahari har bayan rasuwarta. Har yau har gobe tarihinta na nan rubuce a ƙasar nan. Ina son zama kamar ita." Farouk da ya iso kusa da su yana rirrigar Baby Hoodah ya ce, "Ni ma ina miki fatar kasancewa kamar ta Amrah. Insha Allahu za ki zama ɗin, har ma ki zarce ta. Allah ya ba mu ikon riƙo da addininsa, ko kaɗan kar mu zama masu saɓa wa koyarwar ma'aiki SAW." Annur da ke tsaye yana saurararsu duk sai ya ji yaran sun daɗa shiga ransa. Wayo tamkar ba ƴan shekara bakwai ba. Kansa kawai ya gyaɗa bayan ya daɗa yin godiya ga Allah da ya albarkace shi da yaran ƴan biyu, da kuma Hoodah mai sunan Momy Suhailah ƴar watanni biyar. Ya samu Maryama ta fito daga toilet tana duba wasu takardu. Ji ta yi ya riƙo ta ta baya. "Dady ba dai har ka dawo ba." "Na dawo Ammi. Meeting muka yi da wasu baƙi. Sun ɗauke ni contract ne, zan musu wasu zane-zane tsawon watanni uku. Za su ba ni naira miliyan goma." "Alhamdulillahi!" Ta faɗa bayan ta rungumo shi. "Allah ya ƙara buɗi na alkhairi Dady." "Amin ya Allah. Salman sun dawo fa. Kin ji motsin su?" "Ikon Allah! Wallahi ban ji ba. Kuma Hadiza ba ta kira ni ba. Allah dai ya sa sun yi nasara." Shiru ya yi kafin ya ce, "Ba su yi ba Maryam. Wai likitan ya ce bai ga wata matsala a tattare da duka biyun su ba. Lokacin haihuwar ne dai kawai bai yi ba. Daga can ma suka wuce saudiyya suka sake yin addua." "Ehh Hadiza ta ce min dama Saudiyya suka wuce. To Allah dai ya kawo musu mai albarka." "Amin. Saddam dai ya saba sosai da su Farouk." "Wallahi fa. Ko ɗazu Jiddar ta kira ni wai ya Saddam dai ba ya mana kuka ko? Na ce da ita ko kaɗan. Don ma dai Farouk na tsokanarsa ne. Amma dai na masa nasiha insha Allahu ba zai kuma ba." "To madalla. Fiddou ma wai ta sake haihuwa. Gama wayata da Mahmoud kenan na shigo gidan ma." Ta zaro ido. "Lallai Fiddou. Haihuwa ta uku fa kenan. To Allah ya raya mata su bisa sunnah." "Ameen ya Allah. Ya ce wai ni aka yi wa takwara. Annur." Ta ji daɗi sosai. "Aikuwa Dady dole mu daure mu je barka sannan kuma mu koma suna. Sun yi ƙoƙari sosai wallahi." "Allah da gaske sun yi ƙoƙari?" Ta ɗaga kanta. "To sai ke ma ki min ƙoƙari yanzu, ki saukar min da gajiyar nan." Harara ta maka masa. "Su kuma yaran da ke waje mu yi yaya da su?" Ya taɓe bakinsa. "Ke ni fa yara ba su isa su hana ni jin daɗi da iyalina ba. Bari ma ki ga." Ya je ya datse ƙofar da key. Dawowa ya yi gare ta, ya ba ta peck a kumatu, sannan ya ce, "Over to you durling." Daga nan sai abun ya rikiɗe izuwa faranta wa juna rai. Yara na waje an haɗa su da raino, iyayensu na nan suna raya sunnah. ***  Lttle Amrah  Little Farouk and Little Amrah  little farouk and little Amrah  Little Farouk and little Amrah  Little Farouk and little Amrah  Baby Hoodah Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah maɗaukakin sarki. Tsira da aminci su ƙara tabbata ga shugaban halitta annabi muhammadu SAW. Karshen labarin kenan. Inda na yi daidai Allah ya ba ni ladar. Kuskuren da ke ciki Allah ya gafarta min. Karshen labarin AMRAH NAKE SO kenan. Dogon labarin da ya ɗauke mu tsawon lokaci muna yin sa. Fatar masoyana sun ji daɗin sa. Saƙon jinjina ga ƙungiyar NAGARTA. Na gode ƙwarai da haɗin kai da goyon bayanku. Allah ya bar zumunci ya ƙara mana basira baki ɗaya. A ba za ta taɓa tafiya ba sai tare da R da Z. Shi ya sa sunan ba zai tafi da R da Z ɗin nan ba sai tare da A. RAZ abin alfaharina. Mutanen ƙwarai masu matuƙar daraja a gare ni. Ina ƙaubarku da zuciya ɗaya billahi. Ba zan taɓa iya bayyana yadda kuke a cikin zuciyata ba. Amma ku sani, kulluhin rayuwata ta gama mamayewa da ƙaunarku. Allah ya bar mana zumunci har ƙarshen rayuwarmu (Rabiatu sk msh and Zara BB). Ashnur pyar, miemie Queen, Basman mai sanyinta, Meesha, Aunty Maijidda Musa, Ummi Agoss, Asisi Fulanin birni, Zulaihat Rano, Ayshat Modu, Na gode ƙwarai da jimirin bibiyar labarin nan. Wattpadians, ku sani cewa ina matuƙar ƙaunarku. Na ji daɗin yadda kuka bibiyi labarin nan nawa har ya zo ƙarshe. Sai kuma kun ji ni da wani insha Allah. Masoyana: 1 teema💋 2_Kulthoum 3. Matar Sarki 🤴🏻👸🏻 4. Maryam Suleiman😍 5. Fatima Sabo 6.maman iman 7.officialmarcy 8. khairat b umar❤ 9.ruqayya❣ 10•√ fatima muh'd sani {sister sajeedah }💋 11. 💎Najwah💎 12.Khadeejah Musa Yahaya(budurwa) 13.Asmau Attah 14.arousal kois 15. Aysha Ummy 16.Zainab Gwandu 17.Ameena SZ 18. Safura Garba Muhammad 💞 19•Khadeejah ahmad usman(ummy) 20 Nana Hafsat 21•ummu~salmah(ummu~safwan)ut 22.hannat shagari✨ 23. 🌹Hufax🌹 24. Hajara Adam 25. Smart s fawa 26. Ruqayya Sha 28 hauwy❤ 29saudatu Bello Ibrhm 30Khadeeja usman sabo 💞 31 zee h 32.aysha❤ 33.halima amuma(mom mk luv) 34. Lolita 35 Ummu Haidar 36. Asmau Mashee 37 Ummu Aysher 38 Meinerh 39 Fadimatu Dawaki 40. Zainab Liman Tureta. Kuna da yawa, lissafo ku ne babban aiki. Amma ku sani cewa Amrah na alfahari da ku, matuƙar babu ku to babu Amrah. Sannunku da jimirin sharing na wannan labarin. Yan group na RAZ NOVELLA 1&2, Khadija Candy novels, MS INDABAWA GROUP CHART, Pherty novels, Dandalin Bilkisu Bilyamin, Sahaf Novels, Stylish novels group, Asisi Group, Queen Miemie novels Group, MH FANS Group, Mrs. Omar Group, MaryamerhAbdul Fans, House OF Novels Zauren Sadiya novels, Meesha fans group Da duk sauran groups da nake. Na gode da soyayyarku. Tambayoyi: Kun ji daɗin labarin ANS? Me ya fi birge ku a cikinsa? Me ya fi ba ku tausayi har ya zauna a ranku? Wane abu ne ya baƙanta muku rai har ya zauna muku a rai? Wa kuka fi so a cikin labarin? Wa kuka fi tsana a cikinsa? Wa ya fi ba ku tausayi? Wace soyayya ce kuka fi so duk cikinsa? Amrah da Annur? Fiddou da Modu? Jiddah da Deedah? Fiddou da Mahmouda? Ko kuwa ta Marnoor? Tsakanin SHI NE SILAH da AMRAH NAKE SO wane ya fi yi muku daɗi? Me ya sa? Kuna da saƙo zuwa ga marubuciya Amrah? Idan kuna da shi, drop your comments here. Na gode ƙwarai masoyana. Haƙiƙa ba ni da bakin gode muku. Sai dai addua. Allah ya bar mana zumunci ya haɗa mu da alkhairi. Sai kun ji ni a littafi na gaba mai taken GIMBIYA SA'DIYYA (Aljana ko Fatalwa?) labari mai cike da zalunci, ban tausayi, tsoro, soyayya da kuma bayyana wasu abubuwa da suke ba kowa ya san su ba. Instagram: amrah_princess Facebook: Amrah Auwal Email: amratuauwal20@gmail.com Wattpad: PrincessAmrah Snap chart: real_amrah Call, text, Watsapp, Imo, Telegram: 07037603276 Princess Amrah AKA Pinky durling ke muku fatar alkhairi. An dauko wannan littafi daga shafin www.dlhausanovels.com.ng ku ziyarci shafin na www.dlhausanovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from www.dlhausanovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT