[20/11, 19:31] +227 98 36 59 34: 💔 AFIYYA 💔 One (Free page) ✍️ Ayshatuuu 💙 RINGIM, JIGAWA STATE. Taken mu a kullum shi ne " Jinin dabo ringimgim da ka garin karamci" mun amsa wannan taken Dan mu mutane ne masu karamci da dattako, masu riko da alada, garin me ruwa, me kifi Wanda suka San kansu a wajen noma. Bari na barku hakan kada kuce na Koda garin mu da yawa, believe me idan kuka je ringim zaku San ba karya nake ba. Sunana Amina Abubakar Salihu, Amma anyi min lakani da AFIYYA kasancewar na ci sunan kakata data haifi babana ne. Kakana Alhaji Salihu shi ne wazirin sarkin ringim kunga kenan na hada jini da sarauta. Na kanyi tunanin Anya infertility wato rashin haihuwa baya running cikin zuriar mu? Ko Dan ba hakan ya kamata nace ba , zance tabbas infertility na yawo cikin familyn mu. Dukda haihuwar ana yinta sede batada yawa, da anyi daya shikenan, se ta tsaya. Hajiya Amina ita ce kakata, asalinta mutuniyar Ganjin gebi ce. Ita kadai ce matar daya aura Bai Kara Kuma wani auren ba. Yaranta su biyar ne. Mahaifina Abubakar shi ne babba se Wanda ke bi Masa kawu Sa'idu, se Yar tsakiyar su Mummy Maryam, me bi Mata se kawu Ahmad ana ce Masa Tijjani autansu Uncle Salihu amma Babawo ake Kiran shi, my very own savior. Kamar yadda muka sani lokacin da westerners Suka kawo karatun boko an fara dauka ne daga gidajen masarautu Dan a bada misali ga sauran alumma su biyo baya. To mu dinma hakan ce ta kasance lokacin da yaran sarki zasu tafi se aka hada da Babana da Kuma Kawu Sa'idu aka kaisu. Hajiya Bata so saboda tana ganin kamar wani Abu ne ake son koyawa Yara Dan a dauke hankalin su akan turbar musulinci. Da kyar aka samu akai convincing dinta ta amince Suka tafi makaranta, sede kawu Sa'idu fur yaki idan an kaishi se ya gudo ya tafi gidan Gwoggon su dake kyarama, duk kuwa da tsakanin Ringim da kyarama akwai tazara Amma hakan zai gudu. Idan mahaifina ya dawo yayiwa Hajiya complain tayi fada Amma a banza tunda ita Baso take ba Amma tana ganin Dole tayiwa waziri biyayya, Kuma ba zata so yayanta Suki Masa biyayya ba. A haka aka Gama karatun Babu abinda kawu ya tsint, da waziri ya fahimci hakan se kawai ya kaishi kasuwa yace gwara ya nemi abinyi kada ya ja Masa magana a gari. Nanma Babu wani abinda yake illa yaje yayi shawagi ya tafi yawon shi, sede a wañnan shekarar baya ga waccan budurwar baya ga gidan wane, Kuma kowa saboda darajar waziri yake kyale shi. Daddy a kings college dake Lagos anan yayi secondary School din shi, Yana gamawa aka bashi offer Amma se yaki karba akan shi fa se yaje ya Karo karatu. Hajiya Babu yadda batayi dashi ba Akan yayi aure Amma yaki. Haka ta kaishi Kara wajen fulanin sarki se ta nuna Mata itama fama take da nata dan maslaha kawai su kyalesu suyi masu addua. Mahaifiyata sunanta Halima, ban taba ganin ta ba, asalin ta Yar shehun borno ce, akai alliance Akan zaa hada auren yayarta da Baba Mustapha Dan sarki Wanda yake saan Abbuna ne Kuma tare suke karatun acan UK. Yayar ta ita Kuma Mariya, da zasu zo aka saka mamana ta Mata rakiya, bayan an gama komai se sarki yace ai tunda Halima tazo se a hadata da da Abbuna tunda Suma Yan uwa ne. Haka akai aka daura aure mazan na can wata duniya, kowanne se gani yayi an aika Masa da matar shi. Abbu yace min Bai taba ganin mace kyakyawa kamar mahaifiya ta ba, me hakuri da juriya irinta ba. Ya fada min zamansu Zama ne sukai Akan fahimtar juna da soyayya. Shekara na zagayowa Ummin Istanbul kamar yadda muke ce Mata ta haihu Amma mamana shiru ko Bari babu, wannan haihuwar daidai Gama karatun su Suka dawo Nigeria, precisely Ringim, sosae aka tarbesu aka nuna jin dadi musamman haihuwar Ummiey ta dada musu. Anan suka cigaba da rayuwa, Abbuna ya samu aiki a Lagos ga damuwar da mamana ta saka a ranta na rashin haihuwa se aikin yazo Masa da Dadi yasan zata Dan ji Dadi idan tayi nisa dukda bawai takura Mata ake ba, Hajiya me tsananin Kara ce Kuma ta fada min Bata taba suruka ta gari ta kirki me Kara da kawaici who owns a golden heart irin mahaifiyata ba. Baba Mustapha da Ummiey se Suka bar kasar gaba daya, a hakan rayuwa ta cigaba da tafiya. Bangaren Kawu Sa'idu yayi aure matar shi Zinatu, a yawon shi ya samo ta Yar Kano ce Muna kiranta Ummaah, a yanzun bazan ce muku komai akanta ba Amma nan gaba kadan zaku gane irin rawar data taka wajen lalata rayuwata, idan Babu Ummaah cikin labarin AFIYYA to labarin bashi da amfani. Kawu ba karatu yayi ba , shi ba Sanaa yake ba sede standing order da Abbuna yayi Masa duk wata akwai amounts din da yake bashi, dukkan yayan shi Abbuna yake daukar nauyin karatun su. Shi ne kadai Wanda ya haihu da yawa, Ina tunanin kamar ma ya riga Abbuna yin aure. Danshi na farko sunan sarkin Ringim gareshi shi ne aka Kiran shi Baba, na biyu shi ne Yaya, sunan waziri gare shi, bazan taba manta Yaya a rayuwa ta ba, mutum me alkhairi Wanda yaci sunan me sunan shi. Ta uku sunan Hajiya ne da ita ana kiranta Mino, se Siyama se Hafsa. Banda saa a gidan na girmi Hafsa Siyama ta girmeni. Haka yaran shi suke. Mummy Maryam tana auren daya daga cikin yayan sarkin Ringim tana zaune a NY yarinyar ta daya Rukayya muna kiranta Rooks. Kawu Tijjani yana Kano da matar shi Anty Salma, yarsu daya Basma se Uncle Babawo shi ne a UK precisely a Lancashire yake. Shi Bai ma tana haihuwa ba. Abbuna seda sukai shekara ashirin Basu haihu ba, Abbuna yayi kudi,ga ilimi gashi successful business man Amma Babu haihuwa har ya gaji da zuwa asibiti suka fawwalawa Allah. Se at the last minute da suka fitar da Rai sannan kamar Wasa mama ta fara laulayi suna zuwa asibiti akai confirming ciki gareta. Bayan kwana biyu Suka tafi Germany rainon ciki. Kowa yaji labarin cikin se yayi farin ciki Banda Wanda suke adduar Allah yasa kada ta haihu idan Abbuna ya mutu gado nasu ne. Saura sati daya a haifeni waziri ya fara rashin lafiya kamar zai mutu. Dole Abbu ya tafi Nigeria Dan sadawa dashi, Ashe rashin lafiyar ba ta tashi bace kwanan shi daya da zuwa ya rasu. Wanann sakon da ya samu Mama se ya sata ta fara labor, dama tasan cs zaa Mata tunda ta Dade Bata haihu ba. Take aka shiga da ita ot baa fito ba seda sabuwar halitta wato ni! Seda mukai sati daya sannan Abbuna ya dawo jikinta yayi sauki muka dawo Nigeria, a wannan dawowar gaba daya Babu wani dadi, Mama taso waziri ya ganni ya rike no kamar yadda yake Mata nasiha kullum cewar watarana zata hahihu zata dauki danta a hannunta. Se gashi lokaci yayi Amma baya da Rai. Abbu ya saka min Amina, Mummy Maryam ta saka min AFIYYA lokacin tanada tsohon cikin Rooks. Mama Bayan zaman makokin ya lafa ta tafi borno seda ta zubar da wanka sannan ta dawo. Rasuwar waziri ta girgiza mutane sosae nan akazo tunanin Wanda zaa bawa sarauta kowa ya nuna Abbuna yake so Amma se wasu suka nuna ai baya Zama balle a bashi, why not Kawu Sa'idu. Shi dinma so yake a bashi Kuma ace Yana cikin council members na emirate ai yayi gaba kawai. Hakan Bai kasance ba aka bawa Abby shi Kuma se ya wakilta kanin waziri kamar yadda Hajiya ta fada Masa. Wannan abin ya Kara Bata ran Ummaah da kawu Sa'idu. Satin Mama biyu da dawowa muka koma Lagos muka fara sabuwar rayuwa, idan ka kallesu ka kalleni zaka Yi tunanin ni din jikar su ce ba Yar su ba, Dan sunyi girma ace ni din Yar su ce. Na samu gata na samu tarbiya na Kuma samu jin Dadi sede Bai daure ba, Allah ya yanke min hakan ya jefo min wata hanyar da zanbi Dan ya gwada imanina. Shekarata daya Mama tayi rashin lafiya kwananta biyu a asibiti Allah ya Mata rasuwa. AFIYYA is not free! Pay through 3091721807, Aisha Hassan kwalam, First bank of Nigeria (FBN). Send evidence of payment through 09063467258. Ayshatuuu [20/11, 19:31] +227 98 36 59 34: 💔 AFIYYA 💔 Two (Free) ✍️Ayshatuuu Junaidu sunan shi, mahaifin shi Malam Ibrahim Wanda yake haifaffe Kuma zaunannen Kazaure ta jigawa. Mahaifin shi babban malami me Wanda yasan alqur'ani da litattafai. Ko Ina zakaji anyi kwatance da tsoron Allah irin nashi. Sede bawai a malimtar ya tsaya ba shi din manomi ne haka Kuma Dan kasuwa ne Wanda yayi karatu sosae a ilimin zamani, shiyasa malumtar ma take tafiya yadda ya kamata. Allah Yana da hanyoyi da dama na jarabtar bayin shi, duk imaninka baka wuce kaddara, Matan auren shi hudu, Babbar wadda ita ce uwargida Yar Roni ce Hajja Huwaila, ita ta Haifa Junaidu Wanda a yayanta shi ne na uku. Gaba daya yaranta biyar. Me bi Mata ita ce Hasiya wadda Yar nan cikin garin kazauren ce, se ta uku Yar Daura sunanta Fatima, amaryar shi Kuma Yar wani abokin shi ce ya bashi ya aura me suna Sadiya. Gaba daya yaranshi sun tasar ma goma Sha biyar. Yadda aka San gidan malamai gida ne Wanda zaman lafiya da kwanciyar hankali ya yawaita,nan dinma hakane sede idan Mata suka taru Dole akwai abubuwa na kishi da Dan rashin jituwa. A alaadar gidan tun kafin ka Gama primary zakai izu talatin, kana zuwa js3 kayi sauka seka tafi boarding ka cigaba do littatafia. Karatu ana idar da asuba zaa fara, Bayan sallar Isha a daura, Dole kowa se yaje ko ya hadu da fushin malam. Wasu iyayen sun iya banbance yadda yaran su suke tun daga yanayin kukan su suna jarirai da Kuma yadda suke muamula da Yara sa'o'insu idan sun fara girma. Junaidu yaro ne me kuka Yana yaro, kukanshi ya baci, Kuma duk abinda Hajja take ya fara kukan nan se ta katse shi, Yana da zuciya Dan ko an daura shi a po yace ya Gama baa zo da wuri ba to idan akazo tsarki zai ce bazai tashi ba. Cikin dare idan ya tashi Shan ruwa kafin a dakko a bashi yayi fushi bazai karba ba. Wannan halayen nashi yasa ake cewa Hajja tafi son shi saboda gudun zuciyar shi yasa dukkan attention dinta take Kansa, shima Baban wato malam daya fahimci hakan se kullum kafin ya fita se yayi rubutu ya kawo a bashi. A hakan ya fara girma har Yana fitowa waje yayi Wasa da Yara saanin shi dukda ba sosae yake hakan ba Amma duk ranar da ya fita wasan to se ya daki yayan mutane, a gidan su ma idan kannenshi da yayun shi suna Wasa Yana zuwa kowa zai kwashe kayan wasan shi idan ba hakan ba ta kansu zai bi ko Kuma ya dinga wurgi dasu. Kowa tsoron shi yake he's a villain and also a rogue! Primary aka Kai su Amma baya zuwa se ranar da ya ga dama, shi ne shugaban bad gang na cikin makarantar kullum rana idan har suna cikin makarantar to tabbas zasu daki wani ko su sumar da wani. Kullum ana filing complain office din headmaster, har ya gaji ya fadawa Malam halin da ake ciki. Malam ya dawo gida ya aika a Kira Masa Junaidu, ya shigo a nutse saboda haka yake, idan ka kalleshi zakaga zallar nutsuwa a tattare dashi Amma idan ka kalleshi ko ka zauna dashi zaka San Allah ya Masa hallittar nutsuwa shi Kuma ya bijire. Ya tsaya a tsaye Yana cewa Malam gashi yazo,yayan shi Suleiman ya kalle shi ya kalla Malam sannan yace Masa ya nemi guri ya zauna, ko kallon shi baiyi ba balle yasa ran zai zauna hakan ya batawa Suleiman Rai, Yana tashi ya dauke shi da Mari, Amma ko gezau Junaidu baiyi ba se huci kawai da yake Wanda ke nuna ranshi yayi mugun baci, seda malam ya Masa magana sannan ya tsugunna shima yadda tsugunna din kawai se yasa kunyi dariyar takaici. " An kawo min Kara cewar baka zuwa makaranta, idan Kuma kaje kana dukan yayan mutane..." " Inji wanne Dan shegiyar?" Ya fada Yana Kara Bata Rai tareda mikewa tsaye, Suleiman ya Mike yakai Masa naushi a take bakin shi ya fara jini, yasa hannun shi ya lakuto Yana ganin jinin yayi Kan Suleiman ya cakumi wuyan shi ya fara naushin shi, Malam ya Mike da kyar ya raba su, yana sakin Suleiman ya zube a kasa saboda yadda ya karbi naushi a jikin shi, tabbas jikin shi ya fada Masa. Malam ya dafe Kan shi ya kwallawa kanin shi sarki Kira, Babu shiri sukai asibiti da Suleiman. Baa Kara tada maganar ba Amma Malam ya dage da kaiwa Allah kukan shi. Tun daga wanann abun gaba me karfi ta shiga tsakanin Suleiman da Junaidu, Kar kuyi tunanin me sauki basa magana Koda zasu bangaji juna, wannan ya dagawa Hajja Huwaila hankali ya bar Mata abun Fadi wajen kishiyoyi. Lokacin da ya kusa Gama primary se ya fara Shan taba, bakin shi ya fara nunawa, ya daina zuwa karatun da suke na Bayan sallar asuba, ya daina zuwa gaida kowa a gidan, abincin gidan Banda na dare to baya ci. Can wajen kanti akwai wani garejin gyaran mota nan yake zuwa da yamma anan yake samun kudi anan Kuma ya fara Shan taba, da Abu yayi gaba we aka fara bashi Wiwi Yana zuka, baka taba shi da robb da yake shafawa a leben shi da Kuma namijin goro Dan kada kaji warinta. A hankali Malam ya fara gajiyawa da halayen Junaidu se ya fara fita daga alamuran shi. Tun ranar da ya daki Suleiman a ranar Malam ya fara tsoron Junaidu Amma dukda haka yana Masa fada Hajja Huwaila na ma na kokari sosae Akan shi shiyasa ya daina zuwa gidan. Akwai lokuta da iyaye suke samun matsala, itace tun Yana karami ake tankwara shi idan ya bushe zai karye, lokacin da Junaidu ke fatali da kayan wasan Yan uwan shi ya kamata a tsawatar Masa Amma idan yazo ya nayi se Hasiya ta dinga tafi tana cewa ga gwarzo yazo, yanzun zai baza yaran da basa son yin karatu se Wasa kawia Suka sani, ko sun Kai kararshi Huwaila ce kawai zata lallashe su Amma sauran matan se suce ai maganin fitsararru yakeyi. Wannan shi ne abinda ya bashi lasisin yin duk abinda yakeyi, a unguwa ko ya daki Dan wani saboda Malam se kauda Kai, a makaranta baya zuwa Amma form teacher batai reporting ba saboda tana ganin irinsu Junaidu rashin zuwansu yafi zuwan su alkhairi. Kowa ya taka muhimmiyar rawa wajen lalacewar shi, tarbiyyar Bata iyaye kawai bace, ni na yadda cewar tarbiyyar duniya ita ce tarbiyyar, duniya makaranta ce kowa se ta bashi ilimin da yake bukata. AFIYYA is not free, pay 300 into 3091721807, first Bank of Nigeria. A'isha Hassan kwalam. Send evidence thru 09063467258 Ayshatuuu. [20/11, 19:31] +227 98 36 59 34: 💔 AFIYYA 💔 Three (Free) ✍️Ayshatuuu Mutuwar Mama ta girgiza mutane da dama saboda rashin lafiyar da tayi ma ba kowa bane ya San batada lafiya, it was very brief Amma da yake karar kwana ce se gashi ta rasu ta barmu ni da Abbuna. He was completely shattered beyond imagination, har ya koma ga Allah Babu ranar da baya cewa " da Halima nada Rai, Allah sarki Halima" maganar shi kenan, kullum Rana se ya bani labarin ta sede idan baya gari ko bana nan. A luth ta kwanta aka Gama duk wani cike cike da ya kamata sannan yayi booking flight within few hours suka dakko gawar zuwa Kano, kafin mu karaso an turo Mana motoci daga Ringim Emirate council Wanda zasu tafi da gawar zuwa inda dubban mutane ke jira a sallace ta. Abbuna yana rike Dani a kafadar shi tunda muka taho nayi bacci bayan Nanny ta bani oat nasha. Muna zuwa danginta da suke nigeria duka sun biyo flight zuwa Kano sun karasa Ringim, ita mamanta Bata gidan Kuma ita daya ta Haifa, asalin ta Yar Ethiopia ce, so Bayan sun rabu da shehun borno ta koma kasarta, acan Bata wani Jima ba ta rasu, so nidin jini da yawa ke bin veins dina. Ina baccin Nanny ta shiga Dani ta goya ni a wañnan yammacin aka kaita makabarta aka binne ta. Abbu was devastated, kallon shi kadai zai baka tausayi kowa yabin halayen kirkinta yake. Mutane da yawa kallon Abbu Dani ke saka su kuka na tausayin mu. Tunda na farka a baccin aka bani abinci naci se na kankame Nanny dama ni me kowa ce saboda ban Saba ganin mutane a gidan mu ba. Idan Naga mutane Kuma to se na nanike mamata ko Abbuna, idan Babu daya se na nanike Nanny. Kwana uku mutane suka baje yawancin zaman makokin Ina jikin Abbuna a kofar gida Dan naki Zama ciki, kowa se yaji tausayi na. A Rana ta bakwai Bayan an gama adduaa aka raba gado, a cikin dangin Mama Babu Wanda yace zai tafi Dani shima Kuma Abbu Bai yiwa kowa tayi ba, sun tafi suna ta jin rashin dadin rasuwar Yar uwarsu. Duk yadda rayuwa zatayi Dole mutum ya cigaba da rayuwa, duk wani bakin ciki da zaka dandana akwai ranar da zai wuce kaji kamar baayi ba. Bayan gidan ya watse Hajiya tayiwa Abbu nasiha sosae Amma se yace Mata shifa tayi hakuri aure daya ne Kuma yayi Amma baya tunanin zai Kara wani. Mummy tace to ita zata karbe ni ta hada Rooks Amma yace ya gode zai rike ni Yana ganina yaji Dadi. Daga nan muka koma Abuja saboda transfer da akai masa zuwa can. Gidan daga ni se shi se Nanny se Kuma maids din dake Mana aiki, da Nanny ke Mana komai Amma tunda ita ce sabuwar uwata Abbuna ya maida ita kawai kula Dani su Kuma sauran suyi aikin gida. Akai akai yake kaini Ringim Dan na Saba dasu, Yan uwan Mama Babu Wanda ya taba zuwa ya ganni Dan haka Abbu yace shima bazai kaini ba, har na Isa yaye aka daina feeding Dina da Madara se aka koma solid food. Ban Jima da yaye ba na cika shekara biyu, Abbu ya kaini creche, so ni dai as far as am concern tunda nayi wayo a makaranta nake, karatu nake, Dan hakan karatu a cikin Raina yake, shekarata ta farko bani ma da wayo bazan iya tuna komai ba, seda nayi shekara biyar sannan na fara sanin kaina, mutum daya na gane matsayin uwata da ubana Abbu, shi kadai na sani kowa as preliminary nake ganin shi,duk Wanda na Kira da Baba to Kara ce kawai,Dan Babu Wanda ya yimin abinda Abbu yayi min. Saboda yadda na Shiga makaranta da wuri yasa kankanin lokaci na gama. Munje Ringim Ina kwance akan cinyar Hajiya Abbuna ya shigo Dan tun isowar mu fada ya fara zuwa ya gaishe da sarki sannan ya fito mutane Kuma suka tareshi kowa na fada Masa financial complain dinsu Dan ya taimaka musu. Da kyar na yadda na shigo gida shima Yaya na gidan Kawu Sa'idu ne ya lallaba ni muka shigo cikin gidan dashi, Ina ganin Hajiya se na saki hannun shi na nufi inda take zaune ta mike kafafun ta na kwanta Ina ce Mata " I was waiting for you, you didn't come to my house and I missed you!" Ta dungure min kaina tace " Ni bana jin wannan yaran nasarar da Baban ki yake koya Miki, yimin hausa" Yaya dake gefe yayi ta Mana dariya sannan ya fassara Mata abinda nace, ta rungume ni Yana cemin ita ta tsufa ba zata iya zuwa har can capital wajena ba. Tana ta tambayata abinda zanci ne Abbuna ya shigo, nayi saurin tashi na koma kan cinyar shi, murmushi yayi ya zaunar Dani Yana gyara min hular kaina suka gaisa da Hajiya, Yaya ya Mike Dan yasan ya kamata ya Basu guri, hannu ya Mika min yace " So muje na kaiki gidan mu" Na kalleshi sannan na kalla Abbu, ya gyada min Kai tareda mikar Dani tsaye, har na tafi na dawo na rungume shi nace " I'll mish u" Yayi dariya yace " My Princess go" Na wuce hannuna cikin na Yaya muka nufi gidan su dake can gefe duka a cikin Ausar ne. Muna zuwa duka suna zaune ita Ummaah na gaban murhu tana rabon shinkafa da Mai da yaji, su Kuma suna zaune an shimfida katuwar tabarma na bogaji suna jiran a Gama kowa ya dauki nashi. Muna sallama suna ganina Mino ta mike tana fadin " Afiyya oyoyo! Ummaah Kinga Afiyya tazo" Ta juyo ta kalleni ni Kuma naje kamar yadda Abbu yace min idan Naga babba na gaishe shi na tsugunna nace Mata Ina kwana, ta tabe baki ta fara fadin " Kanwar uwarki ce Afiyya da Zaki dinga wannan ihun? Shashasha kawai" Jiki a sabule ta zauna, shikam Yaya Zama yayi yace " Ummaah Baki amsa Mata gaisuwar ba" " To uban shishiggi Kai Kuma, Wai ita wannan Afiyya din Yar gwal ce, bazan amsa ba" Sanin halinta yasa ya guntse bakin shi ya Mike yace min na zauna yanzun zai dawo, na Mike na Kama hannun shi Dan kada ya tafi, Mino yasa ta daukeni haka na Dan zauna a dadare saboda rashin sabo, abinci kowa yaje ya dauki nashi, Nima aka Miko min wani Dan mitsitsi cikin karamin roba, na karba na aje Amma naki ci saboda bana ma jin Yunwa, suna Gama ci Siyama ta janyo nawa ta cinye, Mino na Mata magana Ummaah tace ta barta dama ni na xo na datse musu abincin su. Yaya ya dawo da kifi a Leda ya dauki abincin shi yace nazo naci me kifi, ni Kuma since from childhood bana ketare tayin kifi saboda yadda Abbu ya Saba min cin kifi kullum se mun ci a dinner. Ina ganin Kifin naje na zauna Siyama ma ta taho ya dinga bamu muna ci har ya Gama naje nace ma Ummaah ta wanke min hannu, ruwa kawai ta zuba min na cuda tace naje, nace Mata ai se an saka detergent sanann zai fita, se ta koreni Wai Ina Mata iyayi. Ban wani Kara sakewa ba saboda karnin da hannuna yake na dameshi ya maida ni gurin Abbuna. " Jarabar ka tasa ka dakko ta,seka maida ita ai" Ya Mike ya Kama hannuna muka tafi, Ina zuwa na samu Abbu ya fita, se na zauna wajen Hajiya Ina Mata hirar school, se dare ya dawo da Kifin shi. Naci nayi bacci, bayan fita ta Hajiya ta nuna Masa lallai ya kamata ya kaini maiduguri Koda su Basu neme ni ba to shi ya kamata ya Kai ni na gansu, idan sun cigaba da nemana kansu idan Basu Kara ba shi dai ya sauke wannan nauyin. Washegari muka tafi Kano muka bi flight zuwa maiduguri, ya kaini na gaida kakkani na duk sunata borin kunyar Wai Basu San min koma Abuja ba, se zuzzuta yadda na girma nake Kama da Mama suke. Akazo zau tafi na dinga kuka bazan zauna ba hakan shima ya hakura muka tafi tare. Kawata Dana fara Yi a school namesake Dita ce, sunan ta Amina Abubakar Rogo, gari kadai ya banbanta sunan mu. An tashi school drivern mu duka Bai zo daukar mu ba, muna zaune inda muke Zama mu jira na Bata book Dina Wanda tsayin shi bazai Shiga cikin backpack Dita ba haka itama, inda water dispenser ke aje naje na tsiyayo ruwa nasha sannan nayi discarding cup din sannan na dawo na karba book Dina, kafin na zauna Nanny ta shigo cikin sauri, nayi sauri na nufe ta Ina rungume ta nace " Nanny!" Ta shafa kaina ta karba book Dina, da food box dina da Kuma backpack Dita nayi waving Amina muka tafi. Tun cikin mota nake Mata complain Yunwa nake ji, tace ai ta Gama abinci, nace Mata Abbuna ya dawo tace ai yace se dare zai dawo. Muna zuwa gida na wuce dakina da gudu na dauki waya nayi dialing wayar office din Daddy, Yana picking nace Masa yaushe zai dawo yace nayi hakuri naci abinci zai dawo da daddare, ba yadda naso haka na yadda mukai sallama. Akazo wanka nace ni fa da kaina zanyi da kyar na yadda Nanny tayi min. Ina zaune Bayan maghrib a dakina na tasa drawing book a gaba dasu pencil colors da water color Dole se na zana picture Mama da Abbuna dake rungume Dani on my first birthday, " Where's my princess?" Naji muryar Abbu Yana tahowa dakina, na yadda drawing book din na taho a guje gurin shi na rungume shi, ya daga ni sama ya wulla ni ya cabe nayi dariya na rungume shi. Tare mukaci abinci sannan na raka shi yayi Dan walk cikin compound dinmu sannan Muna dawowa Nanny ta min wanka yazo ya zauna gefena Yana tambayata yadda school ta kasance a hakan nayi bacci sannan ya tafi. Haka yake min kullum indai Yana gida to zai zauna side bed Dina har se nayi bacci. My father my world! AFIYYA is not free, pay 300 into 3091721807 A'isha Hassan kwalam, first Bank of Nigeria. Send evidence of payment through 09063467258. Shatttzzzx [20/11, 19:31] +227 98 36 59 34: 💔 AFIYYA 💔 Four (Free) ✍️ Ayshatuuu Karfe takwas malamin dake zuwa yimin karatun islamiyya yazo, an riga anyi min wanka nan ma se da akai rigima Dani Dan seda Abbu yazo yace yayimin alkawarin ranar birthday Dina ranar Zan fara wanka da kaina, I was super happy na yadda Nanny tayimin , ta shiryani cikin riga da skirt na lace, tea ta bani Nasha sannan ta rakoni parlor na zauna bayan na Gama gaida malamin, gaba daya karatun na one hour ne sannan ya tafi na cire hijab na dawo daki na tafi gurin Abbu. Na samu ya Gama shiryawa for breakfast so a dakin shi muka ci abinci. Bayan mun Gama yace na dakko home work Dina se muyi tare dashi, na wuce dakina na kawo backpack Dita da dayan littafin, Yana dauka yace " Princess wannan ba littafin ki bane ai" Na karba littafin daga hannun shi trying to confirm, dama ban iya spelling Ringim ba amma nasan six letters Suka hada ringim, ni Kuma gashi Naga four letters, sauran sunan irin nawa ne. Nayi shiru se can nace " Abbu canjawa mukai da Amina da Zan Sha ruwa" Ya dafe kanshi sannan Bai ce komai ba ya Ciro waya ya Kira class teacher din mu, ita ce ta fada Masa address din gidan su Amina, yasa Nanny ta canja min casual wears din jikina zuwa wata English gown, aka saka min hula da takalmi, tayimin packing chocolate kamar yadda Abbu yace a bani nakai wa Amina. A garki suke nan muka je, Abbu yayiwa security din bayani, Babu jimawa Sega wani mutum ya fito, Yana zuwa ya gaida Abbu yace mu shigo, Yana fada Masa su Basu ma gane cewar Amina ba book dinta ta kawo ba. Ciki mukaje tana ta Wasa da siblings dinta, seda ta ganni sannan ta taho hade da Jan hannuna nayi Wasa, Dole Abbu ya tafi ya barni a gida se yamma ya dawo ya tafi Dani, that's how Maman Amina ta Zama a figure a cikin rayuwata. Duk Sunday Abbu zai kaini salon, zaa wanke kaina sannan a yanke min farce, ayimin kitso, idan na zauna Baku labarin yadda Abbu ya kula Dani Zan karar da duk wani karfina kafin na shiga gundarin labarin. Abbuna ya min duk wani Abu da uba da uwa zasu min, akwai abubuwan da kake rasawa kake samun makamancin su Amma nikam har na koma ga Allah nasan bazan samu madadin Abbu ba. Rooks cousin dita ce, mahaifiyar ta ita ce Mummy Maryam, kanwa wajen Abbu. Mijinta Dan sarkin Ringim ne Daddy. Tun da ta haifi Rooks ya samu aiki a NY se ya tafi dasu can dama field din daya karanta was international relations. Ban Santa ba se lokacin da nayi birthday Dina na shekara takwas Abbu yace zai kaini Newyork gurin Aunt dina. Banyi wani murna ba saboda ni nafi son kawai na zauna a gida Ina gannin Abbuna. Ya Mana Visa komai dasu passport ya zama ready mukaje Ringim nayi ma Hajiya sallama, se muka biya Kano wajen Uncle Tijjani Abbu ya kaini Naga Basma da Bata wuce 40 days ba. Tunda Naga yarinyar nayi tama Abbu shagwaba Nima se ya siyo min Baby, se da Anty Salma tace min naje idan na dawo zata hada Mata Kaya se na tafi da ita gidan mu. Bamu Kara kwana uku a Nigeria ba muka wuce NY, Mummy tazo airport ta dauke mu, Rooks na makaranta, inata kallon gidan, da dakin Rooks din komai na fulla ne yayi kyau sosae. Na dinga kalla with so admiration a idanuna Ina fatan inama nawa dakin haka yake. Mummy ta shigo tana min murmushi tace " So daughter." Na matso inda take na zauna ta shafa kaina tana ta murmushi tace " Feel at home, Rooks ba zata Jima ba zata dawo. Yaya yaje ya huta zai dawo kinji" Na gyada kaina Ina rarraba idanuna na rashin sabo, abinci ta kirani naci a parlor, Ina fara ci se ga Daddy da Rooks sun dawo, da gudu ta shigo hannunta dauke da backpack dinta, ta rungume ta tana shafa kanta tace Mata " Afiyya tazo" Ta juyo ta kalleni sannan ta kalli mamanta, se Kuma ta wuce dakin ta. Abbu yazo da daddare har lokacin bamu magana da Rooks ba kamar she's not happy nazo gidan su, Abbu washegari ya tafi ya barni shima seda aka fita Dani Dan da ya dawo kuka nayi tayi Bai zo ba. Kwana biyu na sake jiki itama Rooks ta saki jikinta Dani, seda nayi sati uku anan kafin na koma gida,shi ne mafarin sabon da mukai da Rooks. Rayuwa ta cigaba da tafiya, Junaidu har ya Kai matakin shiga karamar secondary, Babu Kuma abinda ya sani haka dai kawai akai gaba dashi ya bar makarantar ko Allah zaisa su huta. Babu jimawa karatu ya kankama nanma ya bude sabon babin iskancin shi, baya zuwa makaranta ko Kuma yazo a makare Kuma kafin a tashi ya sallami kanshi, anan ma ya fara hada gang na bad boys Yana koya musu duk abinda ya iya. Ana haka ya shiga aji biyu daf da karshen term akai fada a gidan su. Ya dawo da yamma ya cake da abubuwan da yake zuka, Yana shigowa gidan Ashe Fatima ta bawa yarta zainab ta siyo Mata kayan Miya, yarinyar wani ya karbe kudin a hanya tana zuwa gida tace ai Junaidu ya karbe kudin. Tunda taji zance tace ai wallahi ko kasa da sama zata hade se an biya ta kudinta ta gaji da dibar albarkar da yake musu a gidannan, jiya ya daki yayanta kawai darajar zaman tare yasa ba tayi magana ba, yau Kuma gashi ya kwace kudi a hannun yarinya, me ake da haihuwar irin su, da kamar Dan Allah bani, inama da akazo haifar shi barin shi akai... Maganganu marasa Dadi Hajja Huwaila na gefe tana bakace ko dago kanta batayi ba balle ta maida martani, a ranta fada take Dan kuka me jawo uwarshi jifa, Hasiya ta fito ta kalla Fatima da har lokacin Bata bar mita ba tace " Ke kuwa kin tabbatar shi Junaidu ya karbe kudin, kinsan yarannan sun iya karya" " To idan bashi ba waye, shi din bako ne a gidannan da ita zainab zata kasa gane fuskar shi?" " Ba bako bane Fatima Amma maganganun da kike fada sunyi nauyi da yawa mahaifiyar shi fa ta nan, ai da kunya" Ta tabe baki yace " Wannan ku ya Dana, tunda ta Haifa se ta bada tarbiyya tunda ta gagara bayar wa se ta bude kunnuwa ta saurari me zamu fada kudina se an biya ni" Kafin Hasiya tayi magana se Suka ji maganar Junaidu a zaure yana fadin " Zan babballa kashin ki wallahi shegiya me Kama da mayu, kin tashi ko Sena hada Miki jini a fuska" Da gudu salama ta shigo, tayi Bayan Fatima wadda ke tsaye tana jiran taga da wa yake, shigowa yayi a lokacin kana kallon shi kasan yasha wani abun, gaba daya idanun shi sunyi jawur tafiyar shi ma Babu nutsuwa, dakin Hajja ya nufa Fatima da ganganci se ta rike Masa riga, " Allah ya Toni asirinka, se ka fito min da kudina kafin na mare ka a gidannan" Ya kalleta sannan ya kalli hannun ta da ta Kama rigar shi ta rike gam yace " Ke dallah sakeni, wanne kudi kike magana anan?" Ya fada Yana kicinayar kwacewa, ta Kara rikewa tana fadin " To meye Dan kace min dallah Naga uwar data haifeka baka gaishe ta, ka Zama Dan shayeshaye meye Dan ka zageni, kudi se ka fiton dashi" Hannun shi yasa ya doke nata yayi gaba abinshi, Amma Bata hakura ba tabi shi ta Kara Kama shi, a zuciye ya juyo Yana juyowa ya hambare ta, aikuwa se gata a zube a kasa, har mamakin karfin Junaidu nake, yayanta sukai kanta, Hajja Huwaila ta mike itada Hasiya sukai kanta, bakinta da hancin ta se jini suke saboda makewar da yayi Mata. Dake salama tafi wayo tana ihu ta tafi ta Kira Malam dake dakin shi, aikuwa ya fito lokacin an maida Fatima daki se kuka take wallahi ba zata yarda ba, Malam ya shigo ya tsaya yayi Shiru ya rasa me zaice saboda yadda zuciyar shi take kamar zata fito ta bakin shi. Hajja Huwaila daki ta koma ta sameshi yayi daidai ya ware fanka Yana bacci, ta daka Masa duka, ya bude idanun shi yayi tsaki ganin ita ce, ya juya Dan gyara kwanciyar shi ta fara fadin " Tashi ka fitar min daki na, kaidao Allah ya wadaran halinka, bakai halin arziki ba San" Dake ba fada ne da ita ba,shi kanshi a sanyaye take fadar hakan. Ya Mike ya nufi tsakar gida zai fita sega Yan sanda sunzo Kama shi Wai Fatima yayanta Ashe DPO ne anan division din Kazaure. Afiyya is not free, pay 300 through 3091721807, Aisha Hassan kwalam, First bank of Nigeria. Send evidence of payment through 09063467258 Shatttzzzx💔 AFIYYA 💔 Five (Free) ✍️ Ayshatuuu DPO ya turo yaran shi akan suzo su tafi da Junaidu, kunsan yadda Yan sanda suke na Nigeria kamar haushi dama suke ji balle Kuma an tabo kanwar DPO Kuma kunsan se inda man su ya Kare, suna zuwa sukai handcuffing din shi Suka tafi dash, mutane suka taru a kofar gidan Dan ganin kwakwaf, malam Yana ciki ya tasa Fatima a gaba ya zuba Mata idanu, ita Kuma ta bawa banza ajiyar shi. Da ya tabbatar ba zatai magana ba se yace Mata " Nayi tunanin hakurin da na baki zakiyi hakuri kiga hukuncin da Zan yanke, Amma kin nuna min kinada Dan uwa" " To Malam Naga kaima dai Junaidu a gidannan ya gagare ka, kana kallon dukan da yayi min da da karar kwana sede a Kira ka ace maka na mutu" Bai ce Mata komai ba ya fito daga dakin nata, Kan shi har juyawa take saboda yadda ran shi yake a bace, dakin Hajja Huwaila ya nufa ya sameta tana kuka Hasiya na gefen ta " Hasiya ni nasan Junaidu Bata jin magana Amma nasan bazai karba kudi daga hannun zainab ba, idan sata ya fara daga dakina zai fara..." Hasiya tace " Yanzun duk wannan ba wani amfani, kizo muje mu samu Malam ayi bailing shi" Ta girgiza Kai tace " A'a gwara a barshi su daka yadda itama Fatima zata ga an Rama Mata, ni abinda ya Bata min Rai Sharron Sara, wallahi Dana haifi barawo gwara ace kaf garinnan yafi kowa shaye shaye" Anan Malam yayi gyaran murya yayi sallama ya shigo, Hasiya ta Masa sannu sannan ta fara kokarin fita ya dakatar da ita, seda ya zauna sannan yace da Hajja " Kukan me kikeyi? Addua Zaki Masa Allah ya shirya ki Amma kukan ki kamar karar shi kike wa Allah" Ta goge hawayen ta amma Bata ce komai ba, ya dubi Hasiya yace ta Masa bayanin abinda ya faru, tiryan tiryan ta fada Masa, ya Gama ji sannan ya fito ya kwallawa zainab Kira, tana dakin Babarta ta fito, yace ta biyo shi daki. Idanunta sunyi raurau ta bi Bayan shi zuwa parlon shi. Seda ya zauna sannan ya fara takbayarta cikin lallami Wanda ya karbe kudin a hannunta, se tace Masa kudin ne Suka Fadi ita Kuma tasan mamanta zata dake ta shiyasa tace Junaidu ne ya kwace. Ya Mata fada sosae akan karya da Kuma husumar data hada a gidan sannan yace ta tafi. Bayan mun dawo daga NY da sati daya na koma makaranta, Abbu ya maida min dakina na Barbie kamar yadda mummy tace mishi, dama naje makaranta ne Ina dawowa Naga har wallpapers duka an canja min, na dinga ihun murna Ina dariyar farin ciki, Nanny na zaune sede tayi murmushi kawai tana kallona. Da ya dawo na rungume shi nace " Abbu kaga dakina yayi kyau, ya koma na Barbie!" Yace min haba dai? Na jashi inata nuna mishi se yace shi ya saka aka gyara min, na Kara rike hannun shi nace " Abbu thank you!" Ya shafa kaina yace idan nayi addua na dinga cewa Allah ya jikan Mama ya Mata Rahma, ban taba manta wannan maganar ba Kuma duk abinda zanyi se na Yi Mata wannan adduar. Da sati ya Kama ne ranar Saturday Bayan islamiyya classes Dina nayi home work, mukai Baki, ban taba ganin su ba so banma sansu ba. Har parlor Abbu ya kawo su Ina zaune kan sofa Ina kallon cartoon din Bob the builder a MBC 3. Suna Zama na gaishe su, daya daga ciki ya dubi Abbu yace " Ta girma Babyn, Allah ya jikan Halima" Abbu yayi murmushi Yana shafa kaina dake gefena ya zauna yace " Lokaci gudu yake Yi ne, gashi ta kusa Gama primary na" Suka gyada kansu in agreement da abinda Abbu yace Suka fara hirar mutuwa, nidai anan nayi bacci jikin shi. " Nasan ba lallai sakon da muka zo maka dashi yayi maka dadi ba, Amma Babu yadda zamuyi muma Yan aike ne" Abbu ya gyara Zama Yana sauraran kawu na, kanin Mama ne " Munyi shawara last week se muka ga ya kamata ace min karbi Afiyya daga gurin ka, she needs a mother's care" Abbu yayi murmushi yace Yana kallona " Afiyya Bata bukatar wannan, nasan ko na amince ku tafi da ita ba zata zauna ba balle ma Nima bazan bada ita ba gaskiya saboda lokacin da nake tunanin zaku karbe ta Babu Wanda yace zai karba, yanzun Kuma ita kadai nake gani na cigaba da rayuwa. Kuyi hakuri Zan dai dinga kawo ta Dan ta Saba daku, Kuma se ku dinga zuwa yadda zata gane ku" " I knew bamu kyauta ba, a lokacin idan mu karbe ta gani muke it will break you more, shiyasa muka bar maka ita, to yanzun ta fara girma she needs a mother ba komai zaka iya Mata ba" Ya girgiza Kai yace " Afiyya needs only me, akanta tasan batada uwa ni ne ubanta ni ne uwarta, bana son na dagula Mata lissafi Kuma. Beside Kun riga kun Yi missing chance din ku na rike ta" Duk yadda sukai Akan Abbu ya Basu ni yaki, they threatened him Amma dukda haka yaki amincewa haka suka tafi ko abincin da aka hada musu Basu ci ba. Wannan shi ne abinda ya fara hada gaba tsakanin dangin mamata da Abbu, su a ganin su duk lokacin da suke so suna da right su karbe ni shi Kuma ya nuna musu akasin haka. Daga wannan se suka shafe batuna cikin rayuwar su Suka manta cewar suna da ya a wani gurin. Shima Abbu se ya tattara su ya kyale su kawai ya zuba musu idanu. Rayuwa ta cigaba da tafiya har na Gama primary school dina. A wañnan hutun Abbu ya dakko Hajiya dani da kawu Sa'idu da Nanny muka tafi saudiyya aikin hajji, acan muka samu Uncle Babawo yazo daga Central Lancashire inda yake msc acan. Tunda yazo kullum zamu tafi harami gurin shi nake zuwa ya rike ni, har Hajiya na cewa Uncle Babawo ya kwace wa Abbu na ni, ni Kuma Kama take min sosae da Abbu, though bani kadai na fada ba, kamar su day Abbu ta baci shiyasa nake son shi, Sabida I see my father in him. Da muka Gama aikin hajji se ni da Abbu muka tafi Paris saboda yayi min alkawarin zai Kai no Naga Eiffel tower. Harda Uncle Babawo muka tafi sauran Suka juya Nigeria. Kwana nan mu uku muka koma Nigeria muma. Nigerian Turkish college nan na samu admission nayi joining Js1 din, har lokacin tare muke da Amina tunda babanta ya tambayi Abbu se yace Masa ai Turkish college zai kaini shima se ya nemawa Amina can muka tafi tare. Baa boarding muke ba day mukeyi, so Abbu se yasa driver kawai yake daukar mu ya kaimu, har gida muke zuwa daukanta mu maida ta, ita Kuma duk ranar Friday Mom dinta zata zo ta dauke mu muje gidan su na wuni. A kwana a tashi kullum rayuwa tafiya take, ni ina Kara girma kamannina suna Kara fitowa da mamana, idan ka ganni sak uwata, komai nata irin nawa ne. Tamkar tayi kaki ta tofar haka nake da ita. Afiyya is not free, pay 300 through 3091721807, A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria. Send evidence through 09063467258 Shatttzzzx💔 AFIYYA 💔 Seven (Free) ✍️ Ayshatuuu Bayan Malam ya Gama sauraron duk bayanan zainab se ya sakata a gaba Suka tafi police station Dan ita kadai ce zata saka ayi bailing Junaidu. Tunda dama it's din ta hada husumar so seta Zama wadda zata warware ta. Lokacinda Suka Isa gaba daya Junaidu ya canja kammanni saboda dukan da ya Sha, tunda Suka shiga DPO yace a lallasa masa shi har se ya gane baa dukan mace. Ga Junaidu da bakar zuciya haka yaki Basu hakuri se amsar dukan yake. Malam na Isa yayi ma officers din dake tsaye a reception bayani, daya daga ciki yace Masa " Malam kawai ka tafi Dan bansan ranar belin wannan gaggararren Dan naka ba" Malam ya gyara tsayuwan shi yace " Idan ba zaku damu ba Ina son magana da DPO din ku" Daya daga ciki yace " DPO baya gari yaje headquarter acan Dutse" Malam ya gyada Kai yace " Idan ba zaka damu ba ko Zan samu num..." " Baya cikin aiki, kaga Malam Muna ganin girmanka a gurinnan, tunda munce ka wuce kawai ka tafi" Malam ya Kama hannun zainab Suka fita a station din, haihuwa kenan sanadin ta Babu abinda bazai same ka ba walau sharri walau khairi, shi Bai taba zuwa police station ba Amma dalilin Junaidu yau shi ake cewa ya fita duk girman shi da darajar shi. " Ai da ka sani ka tatse shi wallahi, malaman nan kudi be dasu, yaran Yan siyasa ne fa" Dayan yace " A'a gwara dai a kyaleshi saboda wannan Yana da connection da manyan mutane kada mu jawa aikin mu" Yana zuwa gidan ya tarar da fada ya barke tsakanin Fatima da Hasiya, Hajja nata kokarin raba su Amma sunki, sede suka hi sallamar shi sannan cacar bakin da suke ta lafa, Bai ce musu komai ba ya nufi dakin shi, Amma kowacce Tasha jinin jikinta, Hajja ta bi Bayan shi ta sameshi zaune ya kurawa guri daya idanu, he looks disturbed. Zama tayi tana fadin " Malam kayi hakuri kada ka Bari abin Junaidu ya dameka, adduar shiriya ita ce zata rabamu dashi" Ya gyada Kai Amma Bai ce komai ba hakan ya tabbatar Mata ba zaiyi magana ba, se ta tashi ta fito dukda tana son taji yadda aka Kare a station din Amma Bata son damun shi, Kuma alamu sun nuna baayi nasara ba, tunda ya shigo babu Junaidu. A tsakar gida taji zainab na fadawa Hasiya yadda sukai a station da officers din, hankalinta ya Kara tashi to Amma ya zatayi? Sai dai ta zubawa sarautar Allah idanu. Wasawasa magana se ta Zama babba tun Malam yana zuwa wajen police din suna Masa yawo da hankali har ya kyalle su, Fatima Kuma sunyi magana da DPO akan se Malam ya Bata hakuri sannan zai sake Junaidu. Ko fahimtar abinda take nufi yayi se ya kyaleta Bai ce da ita komai ba Amma se ya kaurace Mata, kwana biyu da tayi a dakin shi magana ta fatar Baki Bata hada su ba, hankalin ta yayi mummunan tashi, washegari wajen azahar se ga Junaidu an sako Shi, fuskar shi ta kumbura saboda duka, ga jikin shi da duk shatin bulala a jiki. Hajja Huwaila ta daura ruwan zafi tasa yayi wanka, ta gasa Masa jiki sannan ta shafa Masa man zafin da Hasiya ta kawo Mata. Yaci abinci ya kwanta a ranshi Yana saka next abinda zaiyi! Na karasa gaban gadon tareda jijjiga Abbu, Amma a hakan nan dai yake kwance lifeless, Babu digon numfashi dake jikin shi, gaba daya jikin yayi sanyi, kwayar idanun shi a rufe tamkar me bacci, hakan ya tabbatar min daga baccin aka zare Masa Rai. Naja baya da sauri tareda rufe bakina da hannuna Ina jin ilahirin jikina Yana rawa kamar ana kada min mazari. Hajiya na kuka ta fita yayinda ni banyi kukan ba sede Ina tsaye a gaban shi Ina fatan Nanny ta buga min gefen gado na ta tashe ni tace min na tashi zanje makaranta, Amma ba mafarki nake ba, idanuna biyu it's happening in reality Abbu is no more. Nayi shiru ban masan me zuciyata ke sakawa ba a wañnan lokacin, bazan iya Baku labarin yanayin da na shiga ba nasan dai I was more than shattered. Babu wata kalma da Zan muku amfani da ita ta nuna bayyana muku halin da na shiga, Wanda kadai ya rasa iyaye shi zai fahimci me nake nufi. Ina nan a tsaye na fara jin koke koken mutane, Ina tsaye na tsira Masa idanu, Kawu Sa'idu da wasu daga cikin Yayan sarki Suka shigo, duka Ina tsaye aka fara kokarin shiray shi, nasan an ja hannuna an fita Dani, but bazan iya cewa waye ba, kowa kallon shi kawai nake na Zama tamkar statue. Gidan kafin wani lokaci ya cika dam da mutane, se kuka suke Amma gani nake duk yadda suke ji ba zai Kai yadda nakeji ba. Mummy Maryam da Rooks Naga sun shigo, ta rike hannun Mummy dake wani irin kuka tamkar ranta zai fita Amma Ina nikam nawa idanu ne. Seda aka fito dashi cikin makara sannan na Mike tsaye, Kawu Tijjani yazo ya rike hannun na idanun shi se hawaye ke fita yace " So ki Masa addua" Haka na bi bayan shi na zauna gaban gawar, my Father,my love, Abbuna, abokina, uwata da ubana? Shi ne a cikin makara ya tafi, ya mutu Kuma bazai dawo ba. Se na kankame shi na saki wani kuka me daci Ina fadin " Abbu why will you leave me? Bansan kowa ba, you're my everything Abbu ya zanyi rayuwa yanzun..." Na kasa karasawa saboda gaba daya na shide, ban Kara farkawa ba se Bayan awoyi goma da wasu abubuwa sannan na farka a firgice Ina Kiran sunan Abbu, Nanny dake gefena tayi saurin rungume ni a jikinta tana kuka, tana rungume ni nasan ita ce Dan haka na saki jikina na fara kuka bance komai ba Amma radadin da nakeji a cikin zuciyata ya wuce gaban na rubuta muku. Allah sarki Abbu ya tafi ya barni se nake jin inama Nima na mutu na huta, Babu abinda ke tsoratar Dani shi ne na tuna Wai Dole Zan rayu Kuma Babu Abbu. A cikin gida an kaishi makabarta a wañnan yammacin, itama Hajiya tunda aka dawo da abinda aka lullube shi ta mike se kuwa ta yanke jiki ta Fadi, Babu shiri aka dauke ta se Kano asibiti, kafin suje ta rasu itama, Dan hakan mutuwar se ta hade Mana, ga ta Abbu ga ta Hajiya, kowa ka kalla kasan ba karamin blow sakon ya bashi ba, a lokaci guda Allah ya nufi tafiyar su! Rayuwa kenan. Kwana uku gida ya watse Nima aka sallamoni a asibiti , na dawo gidan kowa ya kalleni yadda na rame na lalalce lokaci daya se hawaye ya fita a idanun shi, fada min rasuwar Hajiya ta Kara daga min hankali Amma ban nuna ba Dan ko magana banayi, bana kuka se idan Babu kowa na zauna nayi kuka na share hawayena, a Rana ta biyar Yan maiduguri suka zo, suka Mana gaisuwa, Mummy da Nanny ke kaina wajen tabbatar da naci abinci Kuma Ina nan, wani lokacin ji nake kamar na gudu na fada ruwa Nima ace na mutu da wannan kuncin da nakeji a cikin Raina. Da zasu tafi sukace suna so su tafi Dani nan Mummy ta nuna musu ita zata tafi dani Dan hakan se suka Mana sallama suka tafi, wani lokacin Ina jin inama na bisu may be da duk haka Bai faru ba, to Amma idan na kara wani tunanin se Naga duk abinda ya faru Dani dama is already written in my book, Dole ne ya faru Dani. Ranar sadakar bakwai aka watse ranar nayi kuka Dan Ina zaune kowa ya dinga bajewa sede su shafa kaina su ce min nayi hakuri, nayi kuka na rashin gata, na rashin madafa na rashin sanin yadda rayuwa zata zo min. Abinda kadai ya rage min shi ne Nanny da Rooks. Nanny ta zauna gefena tace " Ki ci abinci kinji, ko so kike kiyi rashin lafiya?" Ina kuka nace " Meye amfanin naci abincin, Abbuna ne ya mutu fa Nanny, banida kowa Nanny" Ta rungumeni tana shafa min baya hawaye itama na bin fuskarta, tausayi na na dawainiya da ita, shigowar Mummy da Uncle Babawo yasa na Mike na nufe shi, ya rike hannuna Yana lallashina, se akai saa nayi shiru har Nasha tea. Fita sukai Shi da Mummy tace " Ina ganin Zan tafi da ita kawai, kallonta is breaking my heart" Ya shafa kanshi Yace " Ita ce abin tausayi Kam, da nayi aure ni Zan dauke ta Amma Zan bar Miki kawai" Washegari Suka zauan meeting akan fate Dina, Mummy ta dubi kawu Sa'idu da mamaki tace " Yaya Sa'idu ni Zan tafi da Afiyya tunda kaga dama ta Saba da Rooks" Ya dago idanu ya kalleta yace " A'a ba zata je gidan wani ta zauna ba watarana ayi Mata Gori ni Zan rike ta" Kawu Tijjani yace " Eh da wannan dukda nasan Daddyn Rooks bazai taba haka ba, dama mafi Dadi ace mu mazan muka riketa. Sede Yaya ka Bari na tafi da ita kawai" Ya Kara Bata fuska yace " Ni Zan rike ta anan Ringim, magana ta kare" Mummy ta hade Rai tace " Yaya Sa'idu in har bazan dauki Afiyya ba to kaima ba zaka dauketa ba, Allah ya gani sede Tijjani ya tafi da ita, ya zaayi yarinya ta tashi a Abuja a dawo da ita Ringim" " Ke wawiya ce Maryam, ke baa Ringim din aka haife ki ba? Mutuwa kikai da Kika girma anan. Kunji maganar banza" Haka dai sukai ta musu aka tashi Babu dadi, Mummy tace musu Dole suyi fighting din Kawu Sa'idu ita Bata yadda dashi ba, washegari da suka je aka raba gadon Abbu, sannan aka raba na Hajiya nan ma yace se de a bashi nawa anan ne Uncle Babawo ya fito da will din Abbu kan dukiya ta ya damka ta a hannun Uncle Babawo haka kawu Sa'idu ya hakura. Bansan me ya faru ba kawai se dawowa sukai sukace Wai a gidan Kawu Sa'idu Zan zauna, Nanny ta bi Mummy dake ta kuka ganin Ina kuka Dan taji me yasa bazan zauna hannun daya daga cikin su ba, Mummy tace itama ba yadda zatayi she can't fight him. Ina ji Ina gani aka tattara kayana duka aka maidani gidan Kawu Sa'idu Kuma yace Nanny ta tafi maiduguri! Afiyya is not free, pay 300 through 3091721807, A'isha Hassan kwalam first Bank of Nigeria, send evidence through 09063467258 Shatttzzzx💔 AFIYYA 💔 Eight (Free) ✍️ Ayshatuuu Cikin kiftawar idanu na rasa koma, mahaifina, gatan da nake dashi da komai na tashi banida kowa da Zan kalla na Kira a matsayin Wanda zanyi kuka a kafadar shi. Ina zaune Nanny ta Gama hada kayanta taxo ta zauna gefena ta rike hannuna cikin barbarcin da take koya min Kuma na dauka sosae Dan duk maganar da zakai Ina ji, Kuma Ina mayarwa sede ba can sosae ba. " Kiyi hakuri nasan komai zai canja, Amma kiyi hakuri kiyi addua, n samu kawun ki Tijjani jiya na tambaye shi tunda Anty Maryam Bata bani amsa ba, yace Yallabai yace su amince da duk hukuncin da kawun ki Sa'idu zai yanke, shiyasa suke Masa biyayya. Ki sani zamanki a gidan shi kamar biyayya kike ga Yallabai, kiyi musu addua Zan dinga zuwa duk lokacin da na samu dama. Ki rike maraicin ki kiyi amfani da illimin ki, kiyi hakuri Allah Yana tare dake..." Nayi ta kuka da hannunta cikin nawa Amma ko sau daya ban manta abinda Nanny tace ba, haka Ina kallo ta tafi ko waiwaye babu, dukda ta hada min kayana tsaf tace da Mummy ita ba zata iya ganina na koma wannan gidan ba. Mummy da yamma ta Gama hada kayan su da Rooks Dan washegari zasu tafi NY, Muna daki na idar da sallar laasar, Rooks ta zauna gefena mukai shiru se can tace " I'm going to miss you Afeey" Na Dan Mata murmushi Amma bance komai ba, ta Kara gyara Zama tace " Promise me duk halin da kike ciki Zaki fada min?" Na Mika Mata hannuna nace Mata na Mata alkawari, shigowar Mummy tasa mukai shiru, ta zauna ya nade kafafun ta sannan tace Rooks ta fita zamuyi magana, haka ta mike ta bamu guri. Mummy ta Jima ta na yimin nasiha wadda na rike ta tsaf sannan tace duk abinda nake so na Kira su zasu bani. Nace Mata to , Bayan maghrib muka shirya se gidan Kawu Sa'idu, na taka zauren da kafata Ina jin kuncin a cikin zuciyata, tun a lokacin na fahimci duniya zancen banza ce, Babu wani Abu da zai daure. Suna zaune an kunna wasu kwayaye Yan kanana an sakale sun haska tsakar gidan, suna zaune akan tabarma Hafsa nata kuka, yayinda Mino ke wanki se Ummaah su na raba abinci, akwatina na da aka kawo tun Rana suna aje a gefe yadda aka barsu, mazan Basu nan. A hankali kamar kwai ya fashe min a ciki na tako na zauna gefen Siyama inda Rooks da mummy Suka zauna, ni na fara gaida Ummaah ta amsa tana cewa Mummy Bari ta karaso. A cikin su Babu Wanda yayi min magana Nima haka, seda ta gama sannan ta dakko kujera ta dawo gefen Mummy ta zauna, nayi jugum Ina bin gidan da kallo, Ina ayyana wacce rayuwa zanyi Kuma a gidan, gidan Kato ne sosae, sede anyi rashin basira a ginin, an bar katon tsakar gida Amma Kuma anyi dakuna biyu kawai se kitchen Wanda bama amfani take dashi ba se bayi guda daya, ta can gefe wajen zauren gidan shi ne dakin dasu Yaya suke ciki, gidan mu na Abuja ya fado min, my spacious bedroom, parlon mu, garden da komai na jin dadin rayuwa. Ina wannan tunanin har bansan sun Gama magana ba se da naji ta taba ni sannan na kalleta ta min alamar na tashi , na kuwa Mike na bi bayanta, Mino ta raka mu dakin, Babu komai se katuwar katifa an gyara ta da bedsheet, daga nan Babu komai, Mummy ta gyara min zaman akwatina na, ta nuna min komai inda yake sannan ta dakko kudi tace min na boye inda ga amfani dashi kadan kadan idan ya Kare zata Aiko min da wani. Ta Kara min nasiha sannan ta tafi ta barni a tsaye a tsakiyar dakin nayi shiru Ina tuna Abbu. Bansan iyakar lokacin da na dauka a tsaye ba seda naji muryar Mino tace min nazo Ummaan su na Kirana, na fito a sanyaye naje na tsaya nace " Gani!" " Dallah samu guri ki zauna" Na koma na zauna aka Miko min Yar karamar silver da tuwo a ciki, na kalla tuwon ban ma gane miyar dake ciki ba saboda abinda aka haska gidan dashi ya fara disashewa, na wanko hannu na saka hannu na tasting miyar first se naji kuka ce, na Dan saki jiki naci Amma se half way naji cikina ya koshi, Dan hakan na tsame hannuna Amma tsoron cewa nake na koshi, se na ta juya hannuna a ciki, se can naji Hafsa da Siyama dake bayana sun fara fada, hankalina haya kansu Amma Ina jin fadan sede ba zance ga dalilin fadan ba, Ina zaune naji Mino tazo kaina tace " Ummaah Bata cinye ba" " Karba ki bawa Hafsa, ni abinda ya rage anan na babanku ne dasu Baba" Nayi saurin cire hannuna tace min " Kin koshi?" " Kar ta koshi Mana, tun karfe nawa na zuba Mata abincin, Wasa ake?" Haka Suka karba abincin Suka bawa Hafsa, na mike na wanke hannuna ina share hawayena na tuna yadda Abbu zai ta lallaba ni har se naci abinci, na wanke fuskata nayi alwala nazo nayi sallah, Ina cikin sallahn naji sallamar Yaya, daga yanayin yadda yake fadin " Ina Afiyya?" Nasan Yana cikin farin ciki, Amma response din Ummaan su ya Sagar Masa da gwiwa " To uban shishiggi, daga shigowar ka ko ni baka tambaya ba se kanwar uwarka Afiyya, gaba daya ku tsaya ki jini man, Afiyya tazo ta zauna bance kowa ya zurfafa muamula da ita ba, bana son kawance ko shishigge mata, ba wata bace, itama ya ce kamar kowa. Ka dauki abinci kaci" Yayi shiru duka suna sauraron ta, Yaya yace " Kai Ummaah, Afiyya abar tausayi ce fa, ya zaai ba zamu jata a jiki ba" " Mhmm kanwar uwarka ba, Dole Ina fada kana mayar min" Baice Mata komai ba ya dauki kwanon shi ya fita, na Jima a zaune sannan nace da Mino dake zaune gefena, " Zanyi bacci, Ina Zan kwanta?" Ta kalleni sannan ta kalla gefen Ummaan su tace cikin kasa da murya " Ko fadawa Ummaan mu" Nayi shiru Ina tsoron tunkarar ta, anan nayi ta guangyadi sauro ya samu ya cije ni son ranshi, se Susa nake, can Siyama ta tashe ni tace naje mu kwanta, haka na Mike nabi bayanta, Ina ayyana yadda zamuyi bacci akan katifa mu hudu, lucky enough Ina zuwa na tarar an Yar min da Yar karamar katifa irin 6x6 dinnan, net ta Mika min na daura, na rike net din Ina tunanin to ya Zan daura, Mino ganin Ina tsaye ta min bayani tana jin motsi tayi shiru, se na fahimci they all want to be nice tsoron iyar su suke. Wani irin dauri na Masa na Shiga na kwanta, gaba daya ya kwanta a fuskata Dan haka da asuba na tashi nayi alwala naji fuskata kamar an zuba Mata barkono, na cije bakina Ina kokarin danne azabar da nake ji, a hakan nayi sallah duk suna bacci Basu tashi ba, gwara Yaya Ina ban daki naji motsin shi. Anan bacci ya daukeni se fadan Hafsa da Siyama ya tasheni, na tashi na cire net din fuskata na azaba kamar zata kwakwabbo, na gaida Mino dake cemin na tashi na kwashe kayan shimfida ta, nace Mata " Kinga fuskata zafi take min" Na fada Ina yatsina fuska, da a gidan mu ne da tuni na tada hankalin kowa kilan se an kaini asibiti, ta taba fuskar tace " Net ne, zai warke kinji" Na gyada kaina, anan ta nuna min yadda Zan saka yau sannan na kwashe kayan muka fito, ta bani tsintsiya Wai nayi shara, na kalla tsintsiyar na kalla tsakar gidan na saki ihu a kaina, Ina neman agaji a gurin Allah! AFIYYA is not free, pay 300 through 3091721807, A'isha Hassan kwalam first Bank of Nigeria, send evidence to 09063467258. ShatttzzzxDake yan class din sun fara lesson a month ago se ya zamana sunyi nisa a physics din, motion shi ne topic din da ya rubuta a jikin board, Amma kafin ya fara bayani Kan motion din seda ya tambayi Yan class Wanda zai iya recapping abinda aka koyar. Sauda dake kusa Dani ta daga hannu, hakan yasa malamin yayi pointing din ta ta tashi ta fara bashi amsa, ta Jima tana bayani kafin Kuma yace ta zauna bayan yasa an tafa Mata. Na kalleta Bayan ta zauna nayi Mata murmushi itama tayimin. Babu dadewa ya shiga bayani Alan motion, nayi shiru Ina assimilating abinda yake fada, haka Ina jotting points where necessary. Seda ya Gama sannan ya mikawa class rep note din yace ta rubuta Mana a board ya fita gaba daya. Na sauke ajiyar zuciya na kalla Sauda nace " Sauda Dan Allah naga note book dinki" Tayi murmushi ta Miko min tace " Amina kinada kyau!" Nayi murmushi kawai Amma ko godiyar compliment din banyi ba, na bude na fara kwafar note dinta, dake inada sauri Kuma Yan class din sun tsaya Wasa ko fara rubuta sabon note din baayi ba yasa na Gama kafin wata period din ta shiga. Nutsuwa nayi inata going through Dan na samu na iya abinda aka koyar. Ina cikin Yi se ga wani malamin ya shigo me maths, wani young guy haka, muka gaishe shi yayi abinda zaiyi ya fita, har lokacin Babu Wanda yayi noticing Dina a ajin, a ranar da aka tashi Sauda ta Ara min books dinta Dan naje na kwafa. Ana tashi na hada books Dina na saka cikin jaka na dubi Sauda na Mata sallama, se sauran dake kusa damu da bansan sunan su ba na musu sallama na fito Ina kallon yadda kowanne dalibi ke kokarin tafiya gidansu, se na tuna tawa rayuwar a NTIC. Na girgiza Kai kawai na fara tafiya a hankali, ga Rana ga zafi ga Yunwa, Amma haka na nufi gida bakina ya bushe saboda kishin ruwa. Tun daga kofar gida na hango Yaya a tsaye Yana magana a waya, cikin sauri na karasa Ina hango murmushi kwance saman fuskar shi, na karasa kafin yayi min magana ko ni nayi ya Miko min wayar shi, na karba na Kara a kunne ba tareda na duba me Kiran ba. " Hello Afeey darling!" Kadan ne Bata kashe min dodon kunne na ba saboda ihun da tayi, na saki dariya a hankali Ina kallon Yaya da ya lumshe idanun shi Yana kallona nace " Rooks! I missed you" Tace min she missed me too sannan tace " So fada min ya makaranta? Yau ranar ki ta farko how do you find it" Tambaya dai a gurin Rooks ba daga nan ba, na zauna kan bencin da Yaya ya janyo min na fara fada Mata komai akan makarantar, a karshe nace Mata " Nafi son waccan ta Abuja, saboda idan na dawo gida Ina tarar da Abbu da Nanny a gida!" Seda na fada naji idanuna sun ciko da kwalla, itama a yanayin yadda tayi min magana nasan jikinta yayi sanyi, na danyi murmushi me ciwo nace " I've to live Rooks ko Dan nayi ma Abbu da Mama addua, I've a reason to live" " Yawwa Afeey, kiyi addua komai zai zo da sauki. Yanzun kin fini class!" Nayi dariya na gama tsokanar ta, cewa ya kamata ta fara Kirana senior, I'm not match for her Dan kuwa na fita aji yanzun. Haka muaki sallama Raina fari Kal, duk gajiyar Dana kwaso se naji ta Dan tafi. Na Mika masa wayar Ina murmushi nace " Thank you Yaya!" Yayi murmushi Yana kallona so intense yace " Ya makarantar?" Na amsa da alhamdulillah sannan nace Masa Zan shiga gida bayan na kara Masa godiya, I felt his eyes trailing on me har na shige gidan. Ina shiga na tarar dukka sun dawo, da sallama na shiga, Mino ta amsa min tana fadin " Ina Kika tsaya?" Na danyi shiru Ina tunanin abinda zanyi cooking, se nace " Mhmm! A hankali na dinga tahowa" Ta gyada kanta na shiga ciki na cire kayana sannan na fito nayi wanka, tunda naji gidan shiru nasan Ummaan su Bata nan, Nima ban tambaye ta ba Dan idan Bata nan gidan yafi Dadi. Abinci muka ci sannan nayi shara na dawo na fara kwafar note, sallamar Ummaan su naji, na daga labule na Mata sannu da zuwa, ta amsa sannan tace na aje littafin nan nazo na Mata wanke wanke, na bude baki da niyyar ce Mata ai nayi tawa sharar tunda dama shi ne aikina, Amma se nayi sealing bakina kawai na tattara littatafan na aje na fito, dogon hannun rigar dake jikina na nannade na hada kayan wanke wanken guri daya na zauna, na fara a hanakli kamar me wanke Raina, nayi nisa ta leko daga daki ta kwalla min Kira, bafa Afiyya take cemin ba sede tace min " Ke!" Shikenan Kuma Dole na amsa, hannuna na dauraye, kafin na karasa dakin naji sallamar Yaya Yana kwalla min Kira, na tsaya tareda juyowa kawai se Naga Nanny a Bayan shi, na cire slippers din kafata na ruga a guje na fada jikinta, na kankame ta kamar Zan koma cikin ta, ta rungume ni itama, na saki dariya wadda take so genuine and sincere nace " Nanny!" Ta Kara rungumeni, bana tunanin Zan manta farin cikin da naji a wannan ranar, da na sake ta Kuma se na fara Kuka me ciwo, na tuna gida na tuna beautiful moments din da mukai tare, na tuna Abbuna. Na rike hannun ta na dinga kuka Ina jin tamkar Ina shading dukkan bakin ciki, da gajiyar Dana kwasa a wannan kwanakin. Ummaan su ta fito dasu Mino dake daki, ta hade Rai tana hararata da ni bama lura nayi ba. Lallashina ta shiga Yi sannan na dakko Mata kujera nace ta zauna, se lokacin ta lura da Ummaan su Suka gaisa ni Kuma na koma kan wanke wanken da nake, Ina wanke wanken Ina Mata tambayoyi tana amsa ni, su kansu nasan Basu taba sanin inada surutu har haka ba. Na Gama wanke wanken tana ta Bina da kallo har na Kai kwanukan kitchen tana zaune, fuskarta na nuna tausayi da Kuma mamakin wata daya yadda na koma wata daban, tana zaune na hura wuta kafin ta Gama kamawa na leka nace da Ummaan su me zaa dafa, tace na Kira Mata Mino na tafi gurin Nanny. Ina Shiga daki da Nanny Sega Yaya, ya shigo hannun shi da Leda ya bani, ruwa ne me sanyi da carbonated drink, nayi murmushi na Masa godiya, na bude Mata na Bata Amma se kallona take, na riko hannunta nace " Nanny naji dadi da Kika zo, kullum se nayi addua ko ke ko Uncle Babawo wani yazo, Allah ya amsa addua ta" Se Naga hawaye suna sauka daga fuskarta, nace " Me yasa kike kuka Nanny, kin tuna Abbuna ko? Ina Masa addua kullum bana mantawa" Ta riko hannuna tace " Me yasa Kika rame? Baki cin abinci ne? Ko aiki kike da yafi karfin ki?" Yarinta ce tsagoro a tare dani, ga wautar Yan fari, ga gabuntar autanci na zauna na fada Mata duk halin da nake ciki, na Kara cewa " Nanny Babu dadi anan, komai Babu dadi, rayuwar gaba daya Babu dadi, dama haka kowa yake komawa idan baban shi ya rasu ko Kuma ni ce Kawu Sa'idu baya so?" Ta girgiza Kai Amma ta kasa magana, se ta rungume ni a jikin ta, mukai sallah, a Jakarta ta fito min da foiled kaza, na kalleta na Kara rungume ta, na zauna naci nayi nak, Dan haka da aka bani jollof din taliya nace na koshi. Guntun lemon da tayi na shanye, wa yaga komai se da dalili Kuma an Dade Baa hadu ba. Ranar bacci nayi me dadin gaske, dukda katifar ta matse mu Amma ban damu ba. Da sassafe kamar kullum na tashi na fita shara na hura wuta sannan na gama nayi wanka na dawo na tarar ta bude akwatina na, ta dubeni tace " Ya akai duk kayan datti a ciki?' Nace " To Nanny bazan iya wankewa ba" Ta gyada kanta kawai, ta fito dasu, wankakkun kadan kawai Suka rage! AFIYYA is not free, pay 300 through 3091721807, first Bank of Nigeria Aisha Hassan kwalam, send evidence through 09063467258 ShatttzzzxNa Gama Shirin makaranta, na kalli Nanny dake juya kayana zuwa daidai nace "Zan tafi makaranta, Amma ba yau Zaki tafi ba ko?" Tace min " Eh ba yau ba, kije ki karba abinci ki wuce" Nace " To Nanny se na dawo!" Haka na dauki jakata na fito tsakar gida, wainar gero aka Miko min naci, nasha ruwa sannan muka tafi cikin ayari. Nanny ta fito da kayan ta fara wanke min, Ummaan su na zaune tana tabe baki dama tun can bawai su nayi da Nanny bane Dan hakan itama Bayan gaisawa da sukai Bata Kara bi ta kanta ba. Tayi nisa a wankin Kawu Sa'idu ya shigo, Dan tun asuba yake fita, yawancin se kowa ya tafi makaranta yake shigowa ya karya sannan ya Kara fita Kuma se dare. Ni kaina bansan wanne irin aiki yake ba, zai fita dai ya dawo, su kule a daki su dinga zance da baka San me sukeyi ba. Ta wanke hannun ta ta zauna kamar yadda ya zauna Yana fadin " Fanta jiya an fada min kinzo, ban shigo gida da wuri ba" Ta danyi dariya tace " Har yanzun anan ana fitar dare kenan?" Yayi dariya shima saboda Mamana tana da Rai takan ce Masa Wai me yakeyi a waje ya Dade har cikin dare? Se yace mata shi baya son sa idanu. " Nazo Naga yata, har an saka ta a makaranta, Allah ya saka da alkhairi ya bar zumunci!" Yayi murmushi jin Dadi yace " Fanta dama Ina Neman ki, naso har karshen sati naje maiduguri na sameki" Nanny ta gyara Zama tace " Akan me fa?" " Akan dukiyar Afiyya ne, bakya ganin ni ya kamata ace nake rike da dukiyar ta tunda ni ke rike da ita?, Amma yaronnan Babawo sede kawai duk wata ya turo min kudi na kula da ita..." Nanny mamaki ya karu Akan nada, dama tunda yace zai rikeni tasan tabbas dukiyar da Abbu ya barmin yake yiwa, to Amma batai Yi tunanin zai iya fallasa abinda yake ji ba. " Wai kana nufin shi Karamin Alhaji Bai baka komai ba?" " Inafa ya bani Fanta? Maryam ce zata Bari ya bani. Tabi ta kankane komai, ni nake wahala da yarinya Basu ba" Nanny ta sauke ajiyar zuciya but ya kamata tasan me yake faruwa, hakan yasa tace " Basu kyauta ba, ai tunda Kai ke rike da ita ya kamata komai nata ace a hannun ka yake, ya kamata ace komai Kai kake kula dashi" Yayi tsaki irin na bacin Rai dinnan yace " Lokacin da akai rabon gado, akwai kadarori wajen uku da yace kada a taba ta Afiyya ce ta makaranta, da wani gida da Kuma wata gona se gidan Mai a Kano, Babawo ko takaddu gurin Bai zo dashi ba, ganin sun tubure ba zasu bani komai ba yasa nace musu kawai sede duk wata su dinga aikon da kudin ciyar watta, shi ne nake tsira da wani abun fa!" To bansan me Nanny ta yiwa kawu ba da har yayi trusting dinta yake bude Mata cikin shi bayan Kuma daga Ummaan su matar shi Babu Wanda ya taba fadawa abinnan, Nanny ranta ya mugun baci, ta rasa ya zata kwantata son zuciyar Kawu Sa'idu, ya takura se ya rike ni, hatta kudin abincin da ba wani abincin arziki ake bani ba se an biya shi, wannan wanne irin rashin zumunci ne, Bayan tasan lokacin da nawa uban nada Rai yayan shi da komai nasu shi ke dawainiya dasu. " Fanta so nake ki lallaba su ko gidan man ne a bani, nasan dukka kowa na ganin girman ki, ke kika go kowa sanin abinda yake akwai, gidan Mai ya dawo hannuna, na Miki alkawarin Zan dinga fitar Miki wani Abu a ciki" Nanny tace " Wannan ba matsala bane, Dana koma zanyi magana da karamin Alhaji" Ya Mata godiya se tace Masa " Me yasa Afiyya baka maida ta can makarantar ta Abuja ba? Bayan suna baka kudin makarantar ta" Yayi dariya yace " Makaranta ai makaranta ce Fanta, ko Ina aka kaika zakai karatu, kinji tsadar makarantar ne ai wannan almubazzaranci ne" Hawaye Suka taru a idanun ta tayi saurin shanyewa ta koma aikin ta, shima ya Shiga ciki Yana jin burin shi Yana daf da cika. Kamar yadda teacher na zaure yayi ma su Junaidu alkawarin da zarar ya cika sharudda ukunnan to kuwan zai ga aiki da cikawa, Yana gamawa ya fice zuwa inda yake koyar aiki, yayi aikin shi se ya tafi majalissar su ya zauna, ya samu dukka suna gurin Dan kaida ce duk yammaci se sun hadu a wañnan gurin. Suna ta Hira suna dariya Malam da Jarma na zuke zuken abinda suka Saba, shi Junaidu ya rage sosae saboda dama influence din su ne, Amma huzaifa Bai ma taba zuka ba shikam Malam he's always the lead. Bayan an gama maghrib kowa ya Kama gaban shi. Fatima ce da girki tun karfe hudu ta kammalla haka take badai kaga tayi Daren girki ba. Ruwa ta tafasa ta shiga wanka, tana watsa ruwan taji wani kaikayi a duk inda ruwan ya sauka, ta dubi jikinta gurin yayi jawur tamkar ta kone, a gigice ta dubi ruwan tasa hannunta Amma shima hannun tana fito dashi se kaikayi yayi jawur, zani ta daura ta fito a guje tana kwalawa Hajja Huwaila Kira, kafin Hajja ta fito tuni Hasiya ta fito ta same ta tsakar gida tana faman sose sosen jiki, Hasiya tace " Fatima ya akai?" Ta kasa magana se nuna Mata take da hannu, tana Susa, lokacin Hajja ta fito itada Amarya suka samu Fatima tana Neman cire zanin jikin ta, ga yaran duk sun zagaye ta wasu a ciki na kuka, hannunta Hajja ta kama Suka shiga daki, Suka fara duba jikinta, duk inda ta Sosa yayi burdi yayi Kuma kwaf kwaf kamar konuwa. Hajja ta Yi shiru Dan ita ta rasa abinda zata ce tunda take Bata taba ganin abin ba, ta dauka hijabi tace da Hasiya " Ke ki zauna da Yara, ni Kuma da Amarya zamuje general, ki aika a fada ma Malam" Da hakan Suka Taya Fatima ta shirya,suka samu Keke napep Suka tafi general, kowa idan aka bude gurin gani suke allergy be hakan yasa focus din maaikatan asibitin, sede ana administering drugs din kamar bama shiga suke ba, in fact tunda jikin ba bukatar su yake ba kokarin reacting musu take. Anan Malam yazo ya same su, hankalin shi ya tashi ganin maaikatan sun ce sede su turasu AKTH suga dermatologist kawai, Malam ya karba takardar, ga Fatima ciwon se Kara Hawa take, se ihu take tana Kiran sunan Allah tana su taimaka Mata kaikayi zai kasheta. A wannan Daren da Junaidu ya dawo ya samu gidan tamkar gidan makokin, yaran na tsakar gida sunyi jugum, Wanda sukai kuka zuwa lokacin sun hakura, Bai bi ta Kan kowa ba ya shige dakin abin shi ya zauna Yana ayyana ya kamata ace zuwa yanzun aikin shi yaci Akan Fatima, tunda kuwa Jarma yace Masa tamkar yankan wuka haka aikin malamin yake, Yana cikin zaune Sega zainab ta leko, tunda sukai abin kudinnan yarinyar ke shishigge Masa tana son ganin ta wanke laifin ta. Yana zaune ta shigo ya dago ya kalleta yace " Meye?!" Ta zauna tace " Mama ce Bata da lafiya!" Ya gyara Zama yace " Me ya sameta?" Ta zauna tana kuka ta fada mishi komai, maimaikon taga ya canja yanayin fuskar shi zuwa tausayi, se taga Yana murmushi, yace " Abin yazo kenan! Kije zata ji sauki" Zainab jiki a sanyaye ta fito ta dawo tsakar gida tayi shiru tana tunanin halin da uwar ta ke ciki, Bata Jima ba suka dawo da Fatima dan a wañnan Daren bazasu iya tafiya Kano ba sede zuwa gobe. Ihun da take yasa Junaidu fitowa kofar daki ya zauna, Bai ce musu kala ba Amma se smirking yake Yana kallon yadda Fatima ta Zama Yar bori, sight din kawai dariya yake bashi, ya zauna yaki tafiya Yana hango duk abinda takeyi, gasu Hajja Huwaila nata karbar jike jiken ayatul shifaa daga gurin Malam, Suka zaunar da ita suka Bata Tasha, Yana shiga cikin ta ta fara amai bakikirin, Hajja ta Kira Malam yana zuwa yace wannan sihiri ne Kuma an karya shi, Hajja ta rike kirji yayinda Hasiya da Amarya suka furta "Sihiri malam!" Ya gyada Kai yace " Tabbas sihiri ne! Allah ya Bata lafiya" Suka saka ta kuskure bakin ta, ta saki ajiyar zuciya ta lumshe idanu bacci ya dauke ta. Malam ya gyada Kai ya juya zuwa dakin shi, daidai dakin Junaidu yaji Yana waya " Man nake fada maka abin yaci fa, dukda dama ba wani tsawon lokaci zai dauka ba Amma nasan ta karbi wahala" Ya Jima Yana sauraron magamganun Junaidu Amma ya kasa gane inda zancen ya dosa, shi yaron tsoro yake bashi tunda Suleiman yace ya ganshi tsakar dare Yana Kona wani Abu a kasko shikenan ya koma jin tsoron shi. Shidai yasan kullum Yana adduar Allah ya shirya yaron Amma Kuma har yanzun abubuwan Junaidu Kara gaba suke. Ranar baccin dadi Junaidu yayi, Dan burin shi ya Gama cika. Da asuba kowa ya tashi yin sallah, seda ya Bari kowa ya fita massalaci, masu Yi a gida sun tayar, ya fito Dan shi ba sallar yake ba se jefi jefi idan ya ga dama. Dakin Fatima ya wuce ya sameta tana kan sallaya tana sallah, ya zauna Kan kujera har ta idar Dan ita Bata lura da shigowar shi ba. Tana idar da sallar ya sakko ya nufo ta, da sauri ta juyo zatayi ihu yace " Junaidu ne!" " Me kake min a daki? Fitar min daga daki nace" Yayi dariya yace " Ba wani Abu nazo nayi Miki ba, daki da kike cewa na fitar Miki daga shi, ai ni Banga daki anan ba. Kinga sakamakon zagi da sharri da Kika min, ko Baki fahimci nine nasa aka Miki sihirin da kikai kaikayin jiya, idan Baki fita harka ta ba Zan saka an Miki wanda Zaki rasa rayuwar ki gaba daya, ko ki haukace, Kuma wallahi zakiyi kyau da hauka.." Yayi dariya ita Kuma tuni jikinta ya fara rawa, tsabar yadda ta tsorata da maganar shi. " Idan kinji shikenan kin tsira idan..." Malam ya bude labulen dakin a zuciye ya Shigo, Fatima da Junaidu lokaci daya Suka Mike, Fatima tayi saurin matsawa gefen Malam Neman kariya, yayinda Junaidu ya tsaya sokoko Yana tunanin abinda zaiyi, Wani Mari Malam ya sauke Masa a saman kuncin sa, yayi baya kamar zai fadi, ya cakumo wuyan shi ya tsayar dashi ya Kara Masa wani, cikin tsananin bacin Rai yace " Ni Dana zaije gurin bokan! Malamin tsubbu! A gidana" Junaidu yayi shiru yana kallon Malam dake janshi har ya kawo shi tsakar gida, dake fadan malam yasa duk sun firfito Dan ganin meke faruwa, duk suna tsakar gidan yasa Sukai carko carko suna kallon Malam da Junaidu a hannu, ga Fatima a gefe se hawaye ke bin fuskarta! Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria send evidence to 09063467258.[15/12, 10:38] +227 98 36 59 34: Junaidu ya runtse idanun shi Yana tuno kalaman malam daya bayan daya, yasa hannun shi ya hargitsa gashin da ya Tara a kanshi, looking like the bad guy he always is, ya sakko da katon akwati ya fara life kayan shi a ciki " Malam kada kayi haka, kada ka yanke hukunci lokacin da ranka ya baci, yawanci idan akai haka a gaba zaayi Dana sani, Kai me fada ne, Kai me bawa Yara tarbiyya ne kada kayi haka Malam!" Hasiya ta fada tana jin kamar ta kurma ihu, Hajja dama tunda taji abinda ya furta ta sulale a gurin ta zauna, saboda tasan matsawar ta cigaba da tsayuwa jirin da take ji zai yadda ita ne a gurin, Kuma ba lallai ta Kara taka kafafunta ba. Malam Bai ce ma Hasiya komai ba yaja hannun Fatima ya maida ita daki sannan ya dawo tsakar gidan, Amarya ta dube shi tana kuka tace " Malam ka sassauta zuciyar ka, ku kuke yiwa mutane waazi akan kada su Bari bacin Rai yayi ruling din su se gashi Kai da bakin ka ka tsinewa Dan da ka Haifa ka Kuma Kore shi daga gidan! Malam" " Na fada Junaidu na fitar shi a cikin Yayana, kada ya Kara waiwayata sannan Kuma kada ya Kara zuwa gidana" Daga haka ya juya ya wuce dakin shi, Hajja ta fara kuka Hasiya na Taya ta, amarya ce me Dan kwarin gwiwar Basu hakuri da lallashin su. Junaidu ya kammalla hada kayan shi tas, ya fara kokarin Jan akwatin Sega Hasiya da Ummiey sun shigo, Ummiey kanwar shi ce, " Yanzun Junaidu baka bawa mahaifin ka hakuri ba, me yasa kake haka?" Ya kakkabe kanshi yace " Ya Dade Bai hakura ba in har ni Zan bashi hakuri. Duniya da Fadi maye ba zaico Kan shi shi kadai ba" Ummiey ta rike hannun shi tace " Dan Allah Junaidu karka tafi, Dan Allah kaje ka bashi hakuri, durkusawa wada ba gajiyawa bane" Ya doke hannunta yace " Ni Zan durkusa na bashi hakuri, ni basamude ne Kinga yazan durkusawa wada kuwa?" Ta share hawayenta tace " Mahaifin ka ne fa, idan ka tafi Ina zakaje" " Ke Wai Ina ruwanki, badai ya koreni ba yaje ai watarana zai neme ni, Baba Hasiya ki kula min da Hajja nagode!" Daga haka yaja kayan shi ya fita ko tsakar gidan Bai kalla ba balle yaje ya ma Hajja sallama, Hasiya ta biyo shi ta rike rigar shi tace " Tafiya zakai? Ba zaka bashi hakuri ba wai!" " Ki Bari Dan Allah Baba Hasiya, kawai Zan wuce ne" Daga haka Bai Kara waiwaye ba ya juya ya bar gidan, duk abin Junaidu da ya fita daga gidan yaga Babu inda zau nufa, garin Babu mutane saboda safiya su Kuma ba Yan uwa ke gare su ba se kawai yaji wani kunci da takaici ya lullube shi. Ya cigaba da tafiya Yana cin buri da alwashi a cikin zuciyar shi, inda Suka Saba Zama yaje ya zauna, shi daya sannan ya fito da bankin shi ya fasa, kudi sosae ya taru a ciki Dan shi mutum ne Mai adani bawai komai ya samu yakai ciki ba. Kamar yasan irin wannan ranar zata zo masa ya dinga Tara kudi, mikewa yayi ya siyo abinci yaci sannan ya dakko wayar shi ya Kira huzaifa yace Masa ya sameshi a gurin su, sannan ya taho da sauran. Nanny kwana biyu ta kara, ranar asabar da safe ta gama Shirin ta zata tafi, tun dare da Naga ta na saka min komai yadda ya kamata kayan data siyo min na fara kuka, ko lallashin na Bata Kara Yi ba ta kyalleni. Na kalleta idanuna sunyi jawur nace " Nanny tafiya zakiyi? Ki tafi Dani Dan Allah Nanny, it's horrible living here" Ta rike hannuna tace " Ni awa Zan tafi dake Afiyya? Zan cigaba da zuwa Ina ganinki inshallah, duk abinda kike bukata kimin waya zansan yadda zanyi a kawo Miki. Karki manta you've to live saboda iyayenki su samu masu musu addua, karki manta da maraicin ki, a kullum ki tuna Allah shi ne gatanki Kuma komai ya faru dake kaddara ce. Naga hisnul Muslim dinki a jaka, na Kara Miki wani kiyi ta addua komai zai zo da sauki ko ba yau ba, akwai ranar da zakiji Dadi!" Na saka kaina a hannunta na dinga kuka, zuciyata ciwo take min, a shekarun da nake dasu kalilan na fuskanci abinda da yawa Basu San Yana wanzuwa ba. " Idan naje maiduguri zanyi magana da dangin Maman ki muga ko zasu zo su dauke ki, sannan zanyi magana da Alhaji karami naji ko akwai abinda zai iya Yi" Nayi saurin girgiza Kai Ina jin bacin Rai Yana mamaye ni nace " Nanny Dan Allah kada kiyiwa kowa magana, ki rabu dasu Dan Allah, a yanzun bana bukatar su. Watarana Nima Zan fita daga halin da nake ciki" Se tayi murmushi me ciwo tace " AFIYYA kada kiyi fushi dasu, akwai abubuwan da a shekarun ki bazaki gane ba,nasan nan gaba Zaki fahimci waye ainahin kawun ki Sa'idu. Kiyi addua sosae Allah zai kawo Miki dauki" Kasa rakata nayi, na tsaya kofar daki nayi ta kuka, Mino da Siyama na tsaye suna kallona da tausayi musamman Mino, Ummaan su dama Bata fito ba, daki sukai sallama, kawu ya leko yayi Mata godiya yace Yaya ya kaita Tasha, ya koma ciki. Har ta Kai zaure se na nufe ta da gudu na rungume ta, na rike hannun ta Ina fadin " Nanny kin yi min alkawarin Zaki dinga zuwa akai akai ko?" Ta gyada min Kai ta share min hawayen dake zarya a kumatuna tace " Kiyi shiru kinji, karki Kara kuka komai zai wuce" Ta dubi Yaya dake a hargitse, idanun shi sunyi ja tace " Me sunan waziri amanar kanwar ka, ka kula da ita Dan Allah" Daga haka ta fita, na Dade a zauren Ina kuka, Babu Wanda yazo ya lallashe ni seda nayi me isata sannan na dawo ciki nayi shara na hada wuta. Nayi wanka na saka Kaya, Yan kayan Dana cire naje na wanke su dukda ba iyawa nayi ba Amma wannan rayuwar da nake ciki ni ce uwata ni ce ubana, Babu me cemin nayi wanki ko akasin haka, ita dai indai nayi Mata aikin ta to idan naga dama ma kada nayi wanka. Inata sakin ajiyar zuciya naji an kwalla min Kira,na fito Amma na kasa magana ta dubeni tace " Bakin ki ciwo yake Miki da Zan kiraki ki ki amsawa?" Nayi Mata shiru kawai, daka min duka tayi a cinya ta tareda dangwarar min da shayi tace " Shegiyar yarinya kawai" Bance komai ba na juya na bar tea din a gurin, ba abinda nake son Sha kenan ba, in fact abinci a wañnan lokacin shi ne Abu na karshe a wanted list Dina, kawai space nake bukata. Na koma daki nayi jugum se jin kawu Sa'idu nayi Yana kwalla min kira, na fito a hankali shima ban amsa ba, Ina tsayawa kawia naji saukar Mari a kuncina, bana tunanin an taba Mari na, idanuna a warwaje na rike gurin na dago na fara kallon shi, kallon da nake Masa na mamaki, tsoro, tsana da Kuma warning, hakan yasa ya daka min tsawa yace " Saukar da idon ki kasa shegiya kawai!" Have you ever felt pain radiating daga zuciya zuwa kowanne sashe na jiki kuwa? Wannan kalma ta shegiya na tsane ta, tafi Marin ciwo a gurina. Naki dauke idanuna yau taurin Kan ya motsa , sede ya motsa inda bazan ci nasara ba. Waya ya dakko ya min duka da ita, na dinga kuka Ina ihu Amma se zagina yake Wai taimko na yake na Isa nama matar sa rashin kunya. Sede yayi min lilis, Mino na gefe da Siyama na kuka. Ya kalleta yace idan na Kara Mata Abu ya Bata go ahead ta dakeni! Anan ko tashi banyi ba na dinga kuka Banda tukuki Babu abinda zuciyata keyi, se jikina da nake jin ya fashe saboda dukan da nasha da cord wire. Ba Wanda ya kulani Dan yaranta tuni ta daka musu tsawa Suka baje, shi Kuma har lokacin Yaya Bai dawo ba. Ina wannan kukan tace naje nayi wanke wanke idan na ga dama na kashe kaina damuwata ce. Haka na tashi naje inayi suka zo suka fice gaba daya sunyi kwalliya Hafsa kayana ne ma a jikinta, shima Babu jimawa ya fita ya rage ni kadai. Ina gamawa na fara maida kayan kitchen, har lokacin hawaye Bai daina sauka ba, mafita kawai nake nemawa kaina. Na shiga kitchen wukar Dana wanke ta silale ta fado seda na aje kwandon sannan na dauki wukar, I began to think ko dai na kashe kaina kawai kowa ya huta, na rike wuakr Ina lumshe idanuna, na saita ta daidai cikina se Kuma na maida ta inda aka cemin major arteries da veins na jiki na gurin wato wuyana, na saka a hankali na furta " Astagfurillah, Abbu Mama I failed you!" Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence through 09063467258. [15/12, 10:38] +227 98 36 59 34: Dake yan class din sun fara lesson a month ago se ya zamana sunyi nisa a physics din, motion shi ne topic din da ya rubuta a jikin board, Amma kafin ya fara bayani Kan motion din seda ya tambayi Yan class Wanda zai iya recapping abinda aka koyar. Sauda dake kusa Dani ta daga hannu, hakan yasa malamin yayi pointing din ta ta tashi ta fara bashi amsa, ta Jima tana bayani kafin Kuma yace ta zauna bayan yasa an tafa Mata. Na kalleta Bayan ta zauna nayi Mata murmushi itama tayimin. Babu dadewa ya shiga bayani Alan motion, nayi shiru Ina assimilating abinda yake fada, haka Ina jotting points where necessary. Seda ya Gama sannan ya mikawa class rep note din yace ta rubuta Mana a board ya fita gaba daya. Na sauke ajiyar zuciya na kalla Sauda nace " Sauda Dan Allah naga note book dinki" Tayi murmushi ta Miko min tace " Amina kinada kyau!" Nayi murmushi kawai Amma ko godiyar compliment din banyi ba, na bude na fara kwafar note dinta, dake inada sauri Kuma Yan class din sun tsaya Wasa ko fara rubuta sabon note din baayi ba yasa na Gama kafin wata period din ta shiga. Nutsuwa nayi inata going through Dan na samu na iya abinda aka koyar. Ina cikin Yi se ga wani malamin ya shigo me maths, wani young guy haka, muka gaishe shi yayi abinda zaiyi ya fita, har lokacin Babu Wanda yayi noticing Dina a ajin, a ranar da aka tashi Sauda ta Ara min books dinta Dan naje na kwafa. Ana tashi na hada books Dina na saka cikin jaka na dubi Sauda na Mata sallama, se sauran dake kusa damu da bansan sunan su ba na musu sallama na fito Ina kallon yadda kowanne dalibi ke kokarin tafiya gidansu, se na tuna tawa rayuwar a NTIC. Na girgiza Kai kawai na fara tafiya a hankali, ga Rana ga zafi ga Yunwa, Amma haka na nufi gida bakina ya bushe saboda kishin ruwa. Tun daga kofar gida na hango Yaya a tsaye Yana magana a waya, cikin sauri na karasa Ina hango murmushi kwance saman fuskar shi, na karasa kafin yayi min magana ko ni nayi ya Miko min wayar shi, na karba na Kara a kunne ba tareda na duba me Kiran ba. " Hello Afeey darling!" Kadan ne Bata kashe min dodon kunne na ba saboda ihun da tayi, na saki dariya a hankali Ina kallon Yaya da ya lumshe idanun shi Yana kallona nace " Rooks! I missed you" Tace min she missed me too sannan tace " So fada min ya makaranta? Yau ranar ki ta farko how do you find it" Tambaya dai a gurin Rooks ba daga nan ba, na zauna kan bencin da Yaya ya janyo min na fara fada Mata komai akan makarantar, a karshe nace Mata " Nafi son waccan ta Abuja, saboda idan na dawo gida Ina tarar da Abbu da Nanny a gida!" Seda na fada naji idanuna sun ciko da kwalla, itama a yanayin yadda tayi min magana nasan jikinta yayi sanyi, na danyi murmushi me ciwo nace " I've to live Rooks ko Dan nayi ma Abbu da Mama addua, I've a reason to live" " Yawwa Afeey, kiyi addua komai zai zo da sauki. Yanzun kin fini class!" Nayi dariya na gama tsokanar ta, cewa ya kamata ta fara Kirana senior, I'm not match for her Dan kuwa na fita aji yanzun. Haka muaki sallama Raina fari Kal, duk gajiyar Dana kwaso se naji ta Dan tafi. Na Mika masa wayar Ina murmushi nace " Thank you Yaya!" Yayi murmushi Yana kallona so intense yace " Ya makarantar?" Na amsa da alhamdulillah sannan nace Masa Zan shiga gida bayan na kara Masa godiya, I felt his eyes trailing on me har na shige gidan. Ina shiga na tarar dukka sun dawo, da sallama na shiga, Mino ta amsa min tana fadin " Ina Kika tsaya?" Na danyi shiru Ina tunanin abinda zanyi cooking, se nace " Mhmm! A hankali na dinga tahowa" Ta gyada kanta na shiga ciki na cire kayana sannan na fito nayi wanka, tunda naji gidan shiru nasan Ummaan su Bata nan, Nima ban tambaye ta ba Dan idan Bata nan gidan yafi Dadi. Abinci muka ci sannan nayi shara na dawo na fara kwafar note, sallamar Ummaan su naji, na daga labule na Mata sannu da zuwa, ta amsa sannan tace na aje littafin nan nazo na Mata wanke wanke, na bude baki da niyyar ce Mata ai nayi tawa sharar tunda dama shi ne aikina, Amma se nayi sealing bakina kawai na tattara littatafan na aje na fito, dogon hannun rigar dake jikina na nannade na hada kayan wanke wanken guri daya na zauna, na fara a hanakli kamar me wanke Raina, nayi nisa ta leko daga daki ta kwalla min Kira, bafa Afiyya take cemin ba sede tace min " Ke!" Shikenan Kuma Dole na amsa, hannuna na dauraye, kafin na karasa dakin naji sallamar Yaya Yana kwalla min Kira, na tsaya tareda juyowa kawai se Naga Nanny a Bayan shi, na cire slippers din kafata na ruga a guje na fada jikinta, na kankame ta kamar Zan koma cikin ta, ta rungume ni itama, na saki dariya wadda take so genuine and sincere nace " Nanny!" Ta Kara rungumeni, bana tunanin Zan manta farin cikin da naji a wannan ranar, da na sake ta Kuma se na fara Kuka me ciwo, na tuna gida na tuna beautiful moments din da mukai tare, na tuna Abbuna. Na rike hannun ta na dinga kuka Ina jin tamkar Ina shading dukkan bakin ciki, da gajiyar Dana kwasa a wannan kwanakin. Ummaan su ta fito dasu Mino dake daki, ta hade Rai tana hararata da ni bama lura nayi ba. Lallashina ta shiga Yi sannan na dakko Mata kujera nace ta zauna, se lokacin ta lura da Ummaan su Suka gaisa ni Kuma na koma kan wanke wanken da nake, Ina wanke wanken Ina Mata tambayoyi tana amsa ni, su kansu nasan Basu taba sanin inada surutu har haka ba. Na Gama wanke wanken tana ta Bina da kallo har na Kai kwanukan kitchen tana zaune, fuskarta na nuna tausayi da Kuma mamakin wata daya yadda na koma wata daban, tana zaune na hura wuta kafin ta Gama kamawa na leka nace da Ummaan su me zaa dafa, tace na Kira Mata Mino na tafi gurin Nanny. Ina Shiga daki da Nanny Sega Yaya, ya shigo hannun shi da Leda ya bani, ruwa ne me sanyi da carbonated drink, nayi murmushi na Masa godiya, na bude Mata na Bata Amma se kallona take, na riko hannunta nace " Nanny naji dadi da Kika zo, kullum se nayi addua ko ke ko Uncle Babawo wani yazo, Allah ya amsa addua ta" Se Naga hawaye suna sauka daga fuskarta, nace " Me yasa kike kuka Nanny, kin tuna Abbuna ko? Ina Masa addua kullum bana mantawa" Ta riko hannuna tace " Me yasa Kika rame? Baki cin abinci ne? Ko aiki kike da yafi karfin ki?" Yarinta ce tsagoro a tare dani, ga wautar Yan fari, ga gabuntar autanci na zauna na fada Mata duk halin da nake ciki, na Kara cewa " Nanny Babu dadi anan, komai Babu dadi, rayuwar gaba daya Babu dadi, dama haka kowa yake komawa idan baban shi ya rasu ko Kuma ni ce Kawu Sa'idu baya so?" Ta girgiza Kai Amma ta kasa magana, se ta rungume ni a jikin ta, mukai sallah, a Jakarta ta fito min da foiled kaza, na kalleta na Kara rungume ta, na zauna naci nayi nak, Dan haka da aka bani jollof din taliya nace na koshi. Guntun lemon da tayi na shanye, wa yaga komai se da dalili Kuma an Dade Baa hadu ba. Ranar bacci nayi me dadin gaske, dukda katifar ta matse mu Amma ban damu ba. Da sassafe kamar kullum na tashi na fita shara na hura wuta sannan na gama nayi wanka na dawo na tarar ta bude akwatina na, ta dubeni tace " Ya akai duk kayan datti a ciki?' Nace " To Nanny bazan iya wankewa ba" Ta gyada kanta kawai, ta fito dasu, wankakkun kadan kawai Suka rage! AFIYYA is not free, pay 300 through 3091721807, first Bank of Nigeria Aisha Hassan kwalam, send evidence through 09063467258 Shatttzzzx [15/12, 10:38] +227 98 36 59 34: Karfe biyu daidai ya tashi daga baccin da yake, lokacin da kowanne Dan Adam dake neman dacewa a wajen mahillicin shi Yana ibada, ko Kuma kowa na kwance na hutawa daga gwagwarmayar da aka Sha da rana, shi Kam Junaidu lokacin ya fito inda yasa salama tun dare ta hada Masa wuta a Mangal yasan zuwa Daren ba lallai ta Gama cinyewa ba, Yana zuwa ya tono anan ya samu har lokacin wutar akwai saura. Ya diba ko tsoro baya ji, baka jin motsin kowa se iska dake kadawa da Kuma karnuka dake haushi, se wild kukan tsuntsaye dake wucewa, ga garin yayi duhu kasancewar watan ya Kai karshe. Ya Gama fifita wutar sannan ya dauka ya shiga dakin sa ya duba lokaci yaga yayi daidai, ya dakko kaso na biyu na maganin ya fara ambulawa a ciki. Hayaki, tukuki duka Suka gauraye dakin, haka ya Gama yayi kwanciyar shi. Da safe ya tashi da wurwuri Dan yasa ran shi zaije makaranta, Dan hakan da wuri ya fita a gidan ba tareda ya nemi kowa ba kamar yadda yasan hajja Huwaila ce kawai zata nemeshi. Yana zuwa makaranta ya zauna bakin aji, ko Ina ya canja Dan yafi wata rabon shi da ya shigo cikin makarantar, idan ka kalleshi ba zaka taba ganin alamar fitina a tare dashi ba, idan ka kalleshi sede ka ga gentle guy with promising future amma a badini bazaka kawo shi ke tantirancin da yake ba. Yana nan zaune har mutane suka fara zuwa, Yan ajin su na asali tuni suna ss2 Amma shi baima San wanne aji yake ba. Yana ta zaune har makamai Suka fara Kora a shiga aji, shima ya Mike kamar na kirki ya nufi aji. Can karshe ya samu ya zauna, Wanda suka lura da zuwan shi a ajin suka dinga zuwa suna gaisawa Kuma suna jajen ya Jima Bai leko ba, sede ya danyi murmushi yace abubuwa ne Suka Masa yawa. Yana zaune sauran gang din shi Suka karaso,suna hango shi suka fara ihu suna hailing din shi, shikam Banda murmushi Babu abinda yakeyi, Jarma yace " Shegen! Amma ko jiya bakace zaka zo makaranta ba" Ya shafa Kan shi da hannu yace " Kawai na tashi naji ya kamata nazo" Malam yayi dariya yace " Wai baka ga admin block Bari daya ya kone ba? Ko ka tambaya" Junaidu ya Dan leka da mamaki ya fara binsu da kallo yace " Guys badai ku..." Bai karasa ba sukaji shigowar principal, sergeant, senior Master da sauran kuso shin school din, sergeant rike da zabga zabgan bulali daga bishiyar maina, kowa a ajin ya tashi in chorus Suka gaishe su sannan, principal yace su zauna, kowa gaban shi faduwa yake kada ma Malam da Jarma suji labari. " It's with dismay that I'm announcing to you the expulsion of some of student in this class. They tempered with the rules and regulations of the school, bullying junior student, coming to school late and leaving school before closure. With all this they went ahead and burnt some part of the administrative block to ashes. Junaidu Ibrahim, Hafizu muhmmad Jarma, Idris yakubu, huzaifa hannafi, I want you out here!" Junaidu ya kalle su duka Suka Mike, malam yace " Guy kace kawai baka nan, Babu yadda zaayi ka karba punishment din mu" Ya girgiza Kai yace " A'a komai tare muke Yi Dan hakan wannan ma tare zamuyi" A tsakiyar makaranta aka saka su sukai lie down flat, sergeant ya dinga dukan su kamar Allah ya Aiko shi, Banda ihu Babu abinda suke, seda bulalaen suka karye kafin kowa aka damka Masa expulsion letter dinsu Suka tafi! Kowanne class ka gani zakaga sun leko suna kallo, Yara da yawa fuskokin su kamar gonar auduga Dan farin ciki. Haka Suka dakko jankunkunan su suka fita daga makarantar jiki duk tsami. Malam ke ta kuka Dan yasan irin nashi iyayen, irin yadda dama suke cin kaniyar shi akan rashin jin shi da Kuma bad guys da yake bi. Shikam goga ko a jikin shi Banda jikin shi dake tsami Amma tun a kofar gate ya faffalla takardar ya yaga, a ranshi yasa tunda aka koreshi to kuwa ya Gama makaranta har abada. Zama sukai suka saka Malam a gaba suka dinga lallashin shi tareda nuna Masa is not necessary se ya fada a gida kawai kullum yayi Shirin makaranta ya taho se suje gareji su koyi aiki, idan time din waec yayi suje wani garin suyi. Da haka ya Dan kwantar da hankalin shi. A bangarena Babu abinda ya canja, kullum wahala Kara Sha nake a gidan, kafin wani lokaci na rame nayi zuruzuru, lokaci zuwa lokaci nakan dauki tab dita idan Babu kowa nayi chatting Maryam. Seda nayi sati na uku sannan ranar Monday da sassafe min tashi kamar kullum. Na kwashe shimfida ta, na fito tsakar gida na dauki tsintsiyar na fara shara, yanzun na iya Babu wannan tsihin, dan Dole ma seda aka saka na koya, seda ya zamana safiya da yamma ni ke shara saboda na kware, ga dundun da Babu fashi matsawar nayi messing Kuma tana gurin. Tun inayi Ina hawaye har ya zamana na ma daina. Na fara shara a hankali kamar yadda yake a jikina, ni ba mutum bace me sauri and I'm not too slow. Na Gama na hura wuta Siyama ta daura abincin safe seda suka Gama wanka sannan ni na shiga a karshe, uniform Dina Mino ta Miko min wani Jan wando farar riga da Kuma Jan hijab, se bakin sandals kwaya daya da stockings daya. Na kalla na kalleta idanuna sun washe nace " Makaranta zanje?" Tana murmushi ta gyada min Kai, na rungume kayan Ina jin Dadi a cikin raina, it doesn't matter to me ko wacce makaranta aka kaini indai Zan cigaba da karatuna that's what matters to me. Cikin sauri na shirya, na dakko body mist Dina da ya rage baifi feshi biyu ba na fesa a hankali sannan na mayar cikin kayana, da tuni na yiwa Abbu dogon list, komai nawa ya kare, Abbu bama ya jira se Abu ya Kare, da zarar wata yazo karshe to Nima zai kaini shopping na saya duk abinda nake so. Na girgiza Kai Ina share hawayen da ya fara min tsartuwa a fuska, na furta "I've missed you Abbuna, Allah ya Kara rahmarsa gareka" Na fito na same su suna karyawa, na zauna na gaida Ummaan su ta dubeni ta tabe baki tace " Meye kike ta dariya da sassafen nan se kace an Miki albishir" Nayi murmushi Wanda inaga tunda nazo it was the genuine smile da na Yi, ta tabe baki ta dangwara min kofin bakin tea din da aka dafa, na karba na fara Sha aka yago min bread na fara ci a hankali, remembering yadda indai bread ne is either toast ko akwai spread din mayonnaise, jam ko chocolate spread Amma ni ce nake yagar shi haka. Har na Saba da abincin da nake ci a gidan, na hakura da komai Dan it's not changing no one is rescuing me. Mun Gama duka muka tashi Dan tafiya, na dauki bag Dita me Asalin kyau tun days Dina na Yar gata, books din kwaya Tara ne Wanda nasan idan js3 ne to tabbas subject din yafi hakan. Kawu ya fito sanye da jallabiyya, na tsugunna na gaishe shi, Suma suka gaishe shi, ya dubeni yace " Uwata se makaranta ko?" Na dago Ina murmushi nace " Eh Kawu" Ya gyada kai Yana murmushi dake Bata min Rai, Dan fuska biyu ne dashi Yadda yake nuna min tamkar Bai masan yadda nake rayuwa a gidan ba Amma ni nasan ya sani, I might be a little naive girl but am not stupid, kwalkwalwata is very sharp, kallonka kawai zanyi I can see through you. " To ayi karatu da kyau" Na gyada Kai na juya na bi bayan su, makarantar da Dan tafiya daga Ausar haka mukaje a kafa, kafin mu karasa ba karamar gajiya nayi ba. Ina zuwa mukaje office din principal ni da Mino, ya dubeni yace " Amma Malam Sa'idu baice min yarinyar karama bace sosae" Mino ta dubeni ta kalla principal din Amma batace komai ba, Dan Bata San yadda sukai da principal da kawu ba. Haka yasa ni a gaba ya kaini class, mutane da yawa a cikin class din, banbancin dake tsakanin makarantar Dana Bari da wannan abin ba zai auni ba. Yace nayi introducing kaina ma Yan class din na fada musu, sannan ya Samar min guri a gaba na zauna, ya Kira wata Sauda yace ta Zama kawata. Na zauna a seat din Ina rarraba idanu a ajin. Yan kusa dani sunata kallona yawanci mamakin kankanta ta suke. Ban Jima ba first period ya shiga, wani malami ya shigo, duka muka tashi Dan gaishe shi ya amsa yace mu zauna, duka muka zauna ya rubuta physics a board, anan na fara wondering kenan ss1 aka kawo ni, ni js3 Zan Shiga fa! Shatttzzzx [15/12, 10:38] +227 98 36 59 34: Na Kara runtse idanuna Ina kokarin dadira wukar a wuyana, many thoughts running through my mind, idan na kashe kaina kowa zai huta, tunda suna ganina tamkar liability ce gare su to gwara kawai na kashe kaina zaifi sauki. Ina dirzawa naji wani irin azabar zafi saboda wukar ko yanka albasa seka dirza balle kashe Kai, na yarda wukar na saki kuka tareda durkusawa a gurin, se Kuma wani tunanin yazo min, idan na kashe kaina Allah a wuta zai saka ni, Ina kallo Mama da Abbu zasu tafi aljanna, I can't be able to reunite with them, ko Kuma Kawu Sa'idu da Ummaan su Mino da ta cuce ni suje aljanna ni da aka cuta saboda na kashe kaina na tafi wuta! Da sauri na Mike Ina girgiza Ina fadin that's not possible I've to live, na dauki wukar na fito tsakar gida, akwai wata tsohuwar rijiya a gidan na jefa wukar ciki, danma kada na cigaba da ganinta suicidal thoughts din Yana zuwa min. Na koma daki na kalla kayana se Kuma na fara tunanin ko dai na gudu ne? Na Shiga duniya kilan na samu wani Mai imanin ya dauke ni! What idan na fada mugun hannu da yafi su Kawu Sa'idu? Na ayyana hakan. Zuciyata se taci galaba a kaina, na bude trolley karama na dauki necessary na saka hijab, I've made my mind I'm leaving this house. Na fito Ina zuwa zaure mukai kicibis da Yaya, ya tsaya Yana kallona Nima Ina kallon shi, hawaye na sauka Kan kuncina, ya kalleni tun daga kasa har sama, mamaki sosae a fuskar shi, ya bude baki zaiyi magana nayi saurin ketare shi Zan wuce Dan ya Gama Bata min budget, hannuna ya kamo hakan yasa na tsaya Ina kicinayar kwacewa, " Ina Zaki je Afiyya? Me ya faru dake? Me akai Miki?" Duka a tare ya jero tambayoyin, na kwace hannuna daga tsatsauran rikon da yayi min, Amma kafin na Kara daga kafata na bar gurin tuni ya rike hijabi na, jawo ni yayi har cikin gidan, inata turjewa Amma seda ya maida ni, na tsugunna a kofar dakin Ina jin shima haushin shi nakeji, kaina kamar zai fado saboda kukan da nakeyi, ga jikina dake ciwo. " Kina ganin idan kin gudu shikenan kin Gama Shan wahala? How will you even think of this? Wa Kika sani Ina Zaki je?" " Ka rabu Dani na tafi, na gaji da wannan rayuwar gwara naje ko Ina ne tunda kowa baya Sona!" " Wayace Miki ba a sonki? Muna son ki mana, ni Rooks and your Nanny, you've to stay for us kinji?" Ya Jima Yana lallashina seda yaga na hakura sannan ya barni yaje ya siyo min abinci a wani eatery ya kawo min naci sannan na shiga daki na kwanta wani bacci me nauyin gaske ya dauke ni. ISTANBUL, TURKEY Daddy ya cire glasses din idanun shi, tamkar cire glass din zai Kara Masa karfin jin sakon da yake amsa ta waya ne, Amma sede maganar da ake Masa tayi Masa nauyi a cikin Kan shi ya kamata yama bada hankalin shi gaba daya akan maganar. " So yanzun Kai a Ina kaji wannan labarin da kake fada min?" Daga dayan bangaren yace " Ranka ya Dade bazan iya fada maka ba Amma yarinyar tana cikin matsala, Alhaji Abubakar Bai cancanci jinin shi yasha wahala ba, shiyasa na Kira na fada maka!". " Wannan hakane na Kuma gode sosae!" Wayar ya kifar ya Mike daga Kan kujera ya Isa jikin suit holder dake gefen shelf dinsa, ya dauka ya zura sannan ya rike kugun shi ya fada tunanin Abbuna, haduwar su ta karshe a ringim ne da sallah yaje gidan shi yake ce Masa " Abubakar me yasa baka kokarin hada Afiyya da Yan uwan mahaifiyar ta" Ya gyara Zama yace "Mariya ta kawo karata kenan?" Abbu yayi dariya yace " Halima ta rasu, ta bar yarinya a kaida tunda princess karama ce to ya kamata su zasu dinga nemanta, Yallabai Babu Wanda ya taba zuwa gidana da sunan sunzo sun ganta, to yazan musu? Ita Mariya ai tana zuwa hutu Ringim, ko yaranku Bata taba turowa ba su ganta, me yasa Bata taba cewa na kawo Mata Afiyya ba. Se yanzun zasui accusing Dina Wai na rabasu da yarsu? Yallabai bazan dinga tura ta gurin su ba suna ganin kamar liability ce, Zan rike yata duk ranar Dana mutu Allah will take care of her" Daddy ya hargitsa kanshi Yana tuna wannan maganar, tabbas Abbu yayi gaskiya laifi Kam nasu ne bana shi ba, ya tuna yayi ma Ummiey magana tace ita ba yadda zatai, shi ya kamata ya dinga neman su Basu su neme ni ba. Runtse idanun shi yayi Yana tuno sakon da aka fada Masa yanzun a waya cewar kwata kwata bana cikin jin dadi, idan ya ganni bazai gane cewa ni ce ba. Cikin sauri ya tattara kayan da zai wuce dasu gida ya fito daga office din. Chauffeur din shi na ganin shi ya karaso da sauri ya karba suitcase din hannun shi, ya bude Masa backseat bayan ya shiga ya rufe, cikin turanci da accent din can yace " Sir where are we heading to?" "Drive me home!" Daga haka ya karkata akalar motar zuwa hanyar gida, lokaci lokaci Daddy Yana picking calls mostly office related calls ne. A yard din gidan yayi packing sannan ya fito ya bude mishi ya fito da wayoyin shi a hannu Yana kashe su Dan kaidar shi kenan, Yana dawowa zai kashe wayar, baya son stress. A parlor ya samu yaran dukka suna zaune, su hudu, babban shi ne sarki na biyu me sunan shehun borno, na uku Harith se autar su Nadia. Gaba daya Babu Wanda yayi aure, sarki ne ma ake zancen nashi da shehu, Amma Harith ba wani shekaru ne dashi ba balle Nadia shekara biyu ta bani. Suna ganin shi Suka Mike kowa da murna kamar kullum Suka tare shi, shehu ya karba suitcase din shi daga hannun chauffeur daya rako shi, bading din su yayi sannan ya juya, " Ina Umminku?" " I'm here Darling! Welcome home" Ta fada tayi kyau cikin gown da akai Mata ado da stones, fuskar ta tamkar an Ciro tata an saka min, dama ance min Kama take da Mamana, Dan wasu Basu ma gane su saboda Kama, Nima na yadda da hakan Dan akwai hoton su na biki a parlon mu da Kuma na ranar sunan shehu Dana suna na. Fuskarta dauke da murmushi tace " Ya aikin you look tired and worried" Ya nufi hanyar dakin shi ta mara Masa baya yace " Ganin ki ya warware gajiyar, lemme have a quick shower" Ta gyada Kai tace ita Kuma zata dakko Masa Kaya kfin ya fito. Bayan sun Gama dinner sunyi Hira da yaran Suka koma daki sukai Shirin bacci, ta zauna gefen gado hannunta dauke da water bottle Tasha wasu pills sannan ta dube shi bayan ta Mata masauki akan bedside drawer ta dube shi ya lumshe idanu ya daura hannun shi akan goshin sa, tasan mijin ta tasan idan yayi hakan Yana cikin damuwa ne, hannunta ta daura akan hannun da ya daura akan goshin tace " Darling how can I help you!" Ya bude idanun shi ya tashi zaune ya dubeta, she looks disturbed also yace " Mariya kin taba tunanin makomar yaran mu Bayan mun rasu kuwa?" Da rashin fahimta tace " Me ya kawo wannan maganar darling?" " Kawai ki bani amsa" Tayi shiru na Dan lokaci kafin tace " Yanzun Babu zumunnci, ba kowa zai rike maka danka ba idan Babu ranka, gata da zaka ma danka shi ne tarbiyya da ilimin addini da zamani" Ya gyada Kai yace " Akwai wayanda sun so suyi hakan Amma Allah Bai Basu dama ba. Kin taba tunanin Ina Afiyya take?" " Wacece Afiyya?" Ya girgiza Kai wani haushi Yana Kara Kama shi yace " Afiyya Yar Halima da Abubakar" Tace " Ooh ai Maryam ta tafi da ita NY ba?" " You failed me Ummin Yara, Baki masan inda Yar Yar uwarki take ba, why? Kin manta tsakanin ki da Halima ne? Afiyya Kun yadda ita Babu me nementa, wallahi Baku kyauta ba" Tayi shiru ta kasa cewa komai itama once in a while hakan Yana damunta, takan tuno yarinyar Amma ta rasa meye yake hanata nemanta. Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence to 09063467258. [15/12, 10:38] +227 98 36 59 34: Na Gama Shirin makaranta, na kalli Nanny dake juya kayana zuwa daidai nace "Zan tafi makaranta, Amma ba yau Zaki tafi ba ko?" Tace min " Eh ba yau ba, kije ki karba abinci ki wuce" Nace " To Nanny se na dawo!" Haka na dauki jakata na fito tsakar gida, wainar gero aka Miko min naci, nasha ruwa sannan muka tafi cikin ayari. Nanny ta fito da kayan ta fara wanke min, Ummaan su na zaune tana tabe baki dama tun can bawai su nayi da Nanny bane Dan hakan itama Bayan gaisawa da sukai Bata Kara bi ta kanta ba. Tayi nisa a wankin Kawu Sa'idu ya shigo, Dan tun asuba yake fita, yawancin se kowa ya tafi makaranta yake shigowa ya karya sannan ya Kara fita Kuma se dare. Ni kaina bansan wanne irin aiki yake ba, zai fita dai ya dawo, su kule a daki su dinga zance da baka San me sukeyi ba. Ta wanke hannun ta ta zauna kamar yadda ya zauna Yana fadin " Fanta jiya an fada min kinzo, ban shigo gida da wuri ba" Ta danyi dariya tace " Har yanzun anan ana fitar dare kenan?" Yayi dariya shima saboda Mamana tana da Rai takan ce Masa Wai me yakeyi a waje ya Dade har cikin dare? Se yace mata shi baya son sa idanu. " Nazo Naga yata, har an saka ta a makaranta, Allah ya saka da alkhairi ya bar zumunci!" Yayi murmushi jin Dadi yace " Fanta dama Ina Neman ki, naso har karshen sati naje maiduguri na sameki" Nanny ta gyara Zama tace " Akan me fa?" " Akan dukiyar Afiyya ne, bakya ganin ni ya kamata ace nake rike da dukiyar ta tunda ni ke rike da ita?, Amma yaronnan Babawo sede kawai duk wata ya turo min kudi na kula da ita..." Nanny mamaki ya karu Akan nada, dama tunda yace zai rikeni tasan tabbas dukiyar da Abbu ya barmin yake yiwa, to Amma batai Yi tunanin zai iya fallasa abinda yake ji ba. " Wai kana nufin shi Karamin Alhaji Bai baka komai ba?" " Inafa ya bani Fanta? Maryam ce zata Bari ya bani. Tabi ta kankane komai, ni nake wahala da yarinya Basu ba" Nanny ta sauke ajiyar zuciya but ya kamata tasan me yake faruwa, hakan yasa tace " Basu kyauta ba, ai tunda Kai ke rike da ita ya kamata komai nata ace a hannun ka yake, ya kamata ace komai Kai kake kula dashi" Yayi tsaki irin na bacin Rai dinnan yace " Lokacin da akai rabon gado, akwai kadarori wajen uku da yace kada a taba ta Afiyya ce ta makaranta, da wani gida da Kuma wata gona se gidan Mai a Kano, Babawo ko takaddu gurin Bai zo dashi ba, ganin sun tubure ba zasu bani komai ba yasa nace musu kawai sede duk wata su dinga aikon da kudin ciyar watta, shi ne nake tsira da wani abun fa!" To bansan me Nanny ta yiwa kawu ba da har yayi trusting dinta yake bude Mata cikin shi bayan Kuma daga Ummaan su matar shi Babu Wanda ya taba fadawa abinnan, Nanny ranta ya mugun baci, ta rasa ya zata kwantata son zuciyar Kawu Sa'idu, ya takura se ya rike ni, hatta kudin abincin da ba wani abincin arziki ake bani ba se an biya shi, wannan wanne irin rashin zumunci ne, Bayan tasan lokacin da nawa uban nada Rai yayan shi da komai nasu shi ke dawainiya dasu. " Fanta so nake ki lallaba su ko gidan man ne a bani, nasan dukka kowa na ganin girman ki, ke kika go kowa sanin abinda yake akwai, gidan Mai ya dawo hannuna, na Miki alkawarin Zan dinga fitar Miki wani Abu a ciki" Nanny tace " Wannan ba matsala bane, Dana koma zanyi magana da karamin Alhaji" Ya Mata godiya se tace Masa " Me yasa Afiyya baka maida ta can makarantar ta Abuja ba? Bayan suna baka kudin makarantar ta" Yayi dariya yace " Makaranta ai makaranta ce Fanta, ko Ina aka kaika zakai karatu, kinji tsadar makarantar ne ai wannan almubazzaranci ne" Hawaye Suka taru a idanun ta tayi saurin shanyewa ta koma aikin ta, shima ya Shiga ciki Yana jin burin shi Yana daf da cika. Kamar yadda teacher na zaure yayi ma su Junaidu alkawarin da zarar ya cika sharudda ukunnan to kuwan zai ga aiki da cikawa, Yana gamawa ya fice zuwa inda yake koyar aiki, yayi aikin shi se ya tafi majalissar su ya zauna, ya samu dukka suna gurin Dan kaida ce duk yammaci se sun hadu a wañnan gurin. Suna ta Hira suna dariya Malam da Jarma na zuke zuken abinda suka Saba, shi Junaidu ya rage sosae saboda dama influence din su ne, Amma huzaifa Bai ma taba zuka ba shikam Malam he's always the lead. Bayan an gama maghrib kowa ya Kama gaban shi. Fatima ce da girki tun karfe hudu ta kammalla haka take badai kaga tayi Daren girki ba. Ruwa ta tafasa ta shiga wanka, tana watsa ruwan taji wani kaikayi a duk inda ruwan ya sauka, ta dubi jikinta gurin yayi jawur tamkar ta kone, a gigice ta dubi ruwan tasa hannunta Amma shima hannun tana fito dashi se kaikayi yayi jawur, zani ta daura ta fito a guje tana kwalawa Hajja Huwaila Kira, kafin Hajja ta fito tuni Hasiya ta fito ta same ta tsakar gida tana faman sose sosen jiki, Hasiya tace " Fatima ya akai?" Ta kasa magana se nuna Mata take da hannu, tana Susa, lokacin Hajja ta fito itada Amarya suka samu Fatima tana Neman cire zanin jikin ta, ga yaran duk sun zagaye ta wasu a ciki na kuka, hannunta Hajja ta kama Suka shiga daki, Suka fara duba jikinta, duk inda ta Sosa yayi burdi yayi Kuma kwaf kwaf kamar konuwa. Hajja ta Yi shiru Dan ita ta rasa abinda zata ce tunda take Bata taba ganin abin ba, ta dauka hijabi tace da Hasiya " Ke ki zauna da Yara, ni Kuma da Amarya zamuje general, ki aika a fada ma Malam" Da hakan Suka Taya Fatima ta shirya,suka samu Keke napep Suka tafi general, kowa idan aka bude gurin gani suke allergy be hakan yasa focus din maaikatan asibitin, sede ana administering drugs din kamar bama shiga suke ba, in fact tunda jikin ba bukatar su yake ba kokarin reacting musu take. Anan Malam yazo ya same su, hankalin shi ya tashi ganin maaikatan sun ce sede su turasu AKTH suga dermatologist kawai, Malam ya karba takardar, ga Fatima ciwon se Kara Hawa take, se ihu take tana Kiran sunan Allah tana su taimaka Mata kaikayi zai kasheta. A wannan Daren da Junaidu ya dawo ya samu gidan tamkar gidan makokin, yaran na tsakar gida sunyi jugum, Wanda sukai kuka zuwa lokacin sun hakura, Bai bi ta Kan kowa ba ya shige dakin abin shi ya zauna Yana ayyana ya kamata ace zuwa yanzun aikin shi yaci Akan Fatima, tunda kuwa Jarma yace Masa tamkar yankan wuka haka aikin malamin yake, Yana cikin zaune Sega zainab ta leko, tunda sukai abin kudinnan yarinyar ke shishigge Masa tana son ganin ta wanke laifin ta. Yana zaune ta shigo ya dago ya kalleta yace " Meye?!" Ta zauna tace " Mama ce Bata da lafiya!" Ya gyara Zama yace " Me ya sameta?" Ta zauna tana kuka ta fada mishi komai, maimaikon taga ya canja yanayin fuskar shi zuwa tausayi, se taga Yana murmushi, yace " Abin yazo kenan! Kije zata ji sauki" Zainab jiki a sanyaye ta fito ta dawo tsakar gida tayi shiru tana tunanin halin da uwar ta ke ciki, Bata Jima ba suka dawo da Fatima dan a wañnan Daren bazasu iya tafiya Kano ba sede zuwa gobe. Ihun da take yasa Junaidu fitowa kofar daki ya zauna, Bai ce musu kala ba Amma se smirking yake Yana kallon yadda Fatima ta Zama Yar bori, sight din kawai dariya yake bashi, ya zauna yaki tafiya Yana hango duk abinda takeyi, gasu Hajja Huwaila nata karbar jike jiken ayatul shifaa daga gurin Malam, Suka zaunar da ita suka Bata Tasha, Yana shiga cikin ta ta fara amai bakikirin, Hajja ta Kira Malam yana zuwa yace wannan sihiri ne Kuma an karya shi, Hajja ta rike kirji yayinda Hasiya da Amarya suka furta "Sihiri malam!" Ya gyada Kai yace " Tabbas sihiri ne! Allah ya Bata lafiya" Suka saka ta kuskure bakin ta, ta saki ajiyar zuciya ta lumshe idanu bacci ya dauke ta. Malam ya gyada Kai ya juya zuwa dakin shi, daidai dakin Junaidu yaji Yana waya " Man nake fada maka abin yaci fa, dukda dama ba wani tsawon lokaci zai dauka ba Amma nasan ta karbi wahala" Ya Jima Yana sauraron magamganun Junaidu Amma ya kasa gane inda zancen ya dosa, shi yaron tsoro yake bashi tunda Suleiman yace ya ganshi tsakar dare Yana Kona wani Abu a kasko shikenan ya koma jin tsoron shi. Shidai yasan kullum Yana adduar Allah ya shirya yaron Amma Kuma har yanzun abubuwan Junaidu Kara gaba suke. Ranar baccin dadi Junaidu yayi, Dan burin shi ya Gama cika. Da asuba kowa ya tashi yin sallah, seda ya Bari kowa ya fita massalaci, masu Yi a gida sun tayar, ya fito Dan shi ba sallar yake ba se jefi jefi idan ya ga dama. Dakin Fatima ya wuce ya sameta tana kan sallaya tana sallah, ya zauna Kan kujera har ta idar Dan ita Bata lura da shigowar shi ba. Tana idar da sallar ya sakko ya nufo ta, da sauri ta juyo zatayi ihu yace " Junaidu ne!" " Me kake min a daki? Fitar min daga daki nace" Yayi dariya yace " Ba wani Abu nazo nayi Miki ba, daki da kike cewa na fitar Miki daga shi, ai ni Banga daki anan ba. Kinga sakamakon zagi da sharri da Kika min, ko Baki fahimci nine nasa aka Miki sihirin da kikai kaikayin jiya, idan Baki fita harka ta ba Zan saka an Miki wanda Zaki rasa rayuwar ki gaba daya, ko ki haukace, Kuma wallahi zakiyi kyau da hauka.." Yayi dariya ita Kuma tuni jikinta ya fara rawa, tsabar yadda ta tsorata da maganar shi. " Idan kinji shikenan kin tsira idan..." Malam ya bude labulen dakin a zuciye ya Shigo, Fatima da Junaidu lokaci daya Suka Mike, Fatima tayi saurin matsawa gefen Malam Neman kariya, yayinda Junaidu ya tsaya sokoko Yana tunanin abinda zaiyi, Wani Mari Malam ya sauke Masa a saman kuncin sa, yayi baya kamar zai fadi, ya cakumo wuyan shi ya tsayar dashi ya Kara Masa wani, cikin tsananin bacin Rai yace " Ni Dana zaije gurin bokan! Malamin tsubbu! A gidana" Junaidu yayi shiru yana kallon Malam dake janshi har ya kawo shi tsakar gida, dake fadan malam yasa duk sun firfito Dan ganin meke faruwa, duk suna tsakar gidan yasa Sukai carko carko suna kallon Malam da Junaidu a hannu, ga Fatima a gefe se hawaye ke bin fuskarta! Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria send evidence to 09063467258. [15/12, 10:38] +227 98 36 59 34: 15 Dukkan su lokaci guda suka Isa Kiran da Junaidu yayi musu, ba karamin mamaki sukai ganin shi zaune da katun katun din jakunkuna, huzaifa ya fara fadin " Me ye wannan? Se kace zaka bar duniyar" Yayi Dan tsaki Yana kallon Malam dake zuge jakar da tafi kusa dashi Dan yaga abinda ke ciki, " Wai korata akai daga wancan gidan" Jarma yace " Wai Malam ya Kore ka kenan? Da gaske?" Harara Junaidu ya watsa Masa yace " Da Bai koreni ba ta Yaya Zan dakko uban kayannan" " Allah ya huci zuciyar ka Man, abinne da bamu kawo ba. Yanzun me zaayi kenan" Ya fada Yana sassauta murya Dan ya lura Junaidu a fusace yake. Jarma yayi shiru yana kokarin tunanin mafita, se can yace " Kai me ka shirya? Meye plan din ka" Yayi murmushi yace " Kudi nake son nayi yadda watarana se sunzo sun nemeni sun nemi gafara ta, sun Kuma nemi kudin abinci daga hannuna" " Wannan haka yake Man, shi ne hukuncin su na yin watsi da kai, da korar ka da sukai. To Amma hakan bazai faru ba se mun nema kudi" Jarma ya gyada Kai yace " Ni na fara jin watarana zaa koremu muma, Dan haka mu je mu karbo saa sannan se mu zo mu fara sanaa mu Gina kanmu!' Da wannan shawarar Suka tafi can shagari Suka sama Masa shago na haya, suka biya kudi seda yayi settling kafin suka fita Suka barshi Dan sun fahimci Yana son kebewa. Kwanciya yayi ya lumshe idanun Shi ya fara tunanin yadda zaiyi yayi kudi ya dauki fansa! Kwana biyu na daina shiga harkar kowa a cikin gidan, hatta su Mino da muke Dan magana dasu na daina, aikin duk da nasan nawa ne ni zanyi tun kafin ace nayi na tashi nayi, duk yadda take kokarin ganin ta dakeni batada wani dalilin dukan, abinci idan an bani naci idan baa bani ba na hakura Nasha ruwa. Yaya kadai nake ma magana, Amma shi kanshi Kawu Sa'idu da naji muryar shi Zan koma daki Dan Kar ma mu hadu, shima Bai tambayi inda nake ba. Na fito daga wanka naji ciwo a marata, na cigaba da daurewa na saka uniform, na dauki madubi Ina kallon fuskata, Ina cikin mutane masu doguwar fuska, oval shape, ni ba fara bace fatata me duhu ce dukda duhun ba can can ba Amma nasan kala biyu Allah ya halitta fari da baki, Babu wani tarwada Dan hakan ni baka ce, inada gashi Dan banida goshi, kusan gashina har girata ya hadu, idanuna suna da haske da hakorana, farare ne tas, hakorana Yan kanana a jere se dimple da nake dashi Wanda ba se nayi dariya ba yake lotsawa ba, ko magana nayi zakaga ya lotsa, wannan shi kadai ne marabata da Mama, Hajiya tace min ita batada dimples Amma Ummiey na dashi. Na Kara kallon madubin Ina ganin yadda idanuna sukai kwala kwala saboda yadda duk na rame, hancina ya Kara kankacewa dama ni banida hanci, haka yake Dan dus, kumatuna duk sun zagwanye. Na lumshe idanuna Ina ayyana abubuwa da dama a cikin zuciyata. Mino tace min " Zaki makara fa Afiyya, ki tashi ku tafi" Ita ta fara neco so ba kullum take fita ba, na Mike bance Mata komai ba na zura hijab na dauki jakata na fita tsakar gida, na samu suna cin wainar flour da aka soya da safiyar. Ta kalleni tace " Kizo ga Taki" Na Isa gurin na dauka Naga kwaya daya ce kamar ma irin kalen robar ne da ya rage aka soya min, wani Abu yazo wuyana ya tsaya, kamar na wurgar nace ba zanci ba Amma se na tuna dukan da naci cikin satin, hakan yasa na zauna na cinye na goge hannuna sannan nace na gode muka fita. Yaya ma samu a kofar gida Yana zaune Kan wani bench dake gurin Rai da rai, ya Mike ganin mu. Siyama ya mikawa naira dari yace ta siya Abu ta siyawa Hafsa, karba tayi ta ja hannun Hafsa suka wuce. " Have you eaten?" Ya fada Yana zura hannun shi cikin aljihun wandon jikin shi, nayi murmushi tareda gyada Kai, ya jinjina Kai yace " Kinyi azkhar? Amma face dinki looks disturbed" Nayi saurin shafa fuskata tareda Kara yin murmushi nace " Yes and I'm fine" Se yayi shrugging shoulders din shi ya Miko min dari biyu yace " Karba ki tafi, nasan Baki ci abinci ba, use this to buy something and I won't take no for an answer!" Ya zanyi hakan na saka hannuna na karba na mishi godiya, na juya Ina jin wani sanyi Yana ratsa min jikina, da zuciyata, na saki murmushi daidai jin an Kira sunana, juyawa nayi na ganshi a tsaye ya harde hannayen shi a kirji Yana kallona a sanyaye Yana murmushi, na tsaya tareda tsare shi da nawa idanun, ya matso inda nake tsaye yace " You're beautiful Afiyya, I love your dimples and..." Se na rufe fuskata da tafikan hannuna Ina sakin karamar dariya wadda shi dayake jinta seda ta narkar Masa da zuciya har ya gagara karasa abinda yayi niyyar fada. Juyawa nayi da sauri na nufi makaranta, Amma kunnuwana se echo muryar shi suke min na abinda ya fada, lokaci lokaci se na shafa dimples din nawa na saki murmushi. Ina zuwa gate Naga an fara Taran makara, na karasa Naga su Siyama ne Dan ita tana ss2 Kuma tunda Babu ss3 Dole su zasui taking charge, tsuggunawa nayi kamar yadda kowanne late comer ya tsugguna, daga can naji Siyama a gefena tana fadin " Ina Kika tsaya? Yaya ne ya tsayar dake ko?" Na gyada Mata kai, tuna sunan shi sena fara picturing fuskar shi Yana min murmushi, nayi saurin runtse idanuna Dan na bar ganin fuskar shi. A cikin prefect din naji wata tana cewa Siyama " Har yanzun wadda Kika daukarwa excuse din Bata zo ba?" Siyama ta kalleni sannan tace " Gata tazo" Ta fada tana nuna musu ni, a take akace na wuce class, na kalli Siyama na Mata Murmushin godiya sannan na wuce class na samu malamin English din Bai riga ya shiga ba, na sauke ajiyar zuciya na zauna gefen Sauda dake fama da phrasal verb cikin comprehensive passage, " Yawwa Amina Abubakar tun dazun nake jiranki, me yasa Kika makara yau?" Na Mika Mata hannu mukai musabaha nace " Ki Bari kawai, surutu na zauna Yi" Tayi dariya tace " Ke da har surutu kike? Lallai Kam! Kinga duba min wannan kamar adverbial phrase ko?" Na gyada Kai daga haka na shiga nuna Mata na time, na place da sauran har malamin ya shigo. A tsaye Dana bar Yaya, Bai matsa ba ya cigaba da bin bayana da kallo har na kulle ya shafa Kan shi tareda Ciro wayar shi dake ringing cikin aljihu, baikai ga picking ba yaji muryar abokin shi Nuhu Yana fadin " Naga dalilin palpitations yau" Yaya ya daga kanshi Yana Sosa Kai ya dubi Nuhu dake dariya kasa kasa yace " Doctor! Me kake nufi" Ya samu guri ya zauna, shima Yaya ya zauna Suka gaisa sannan Nuhu ya dubi Yaya yace " Engr. Kwanaki ka kirani akan kana tuannin kamar heart failure na damun ka?" Yaya ya shafa Kai yace " Eh lokacin gaba daya yadda kasan ana farautar rayuwata ne, Ina jin yawan faduwar gaba matsananciya, wani lokaci har haki nake fa, but yanzun na daina ji" " Haka kurum kake hakan ko se kaga wani Abu?" How is he supposed to start saying se ya ganni sannan wannan symptoms din ke zuwa, Dr Nuhu yace " I guess waccan yarinyar ita ce dalili ko?" Ya kalle shi da sauri Yana kokarin musawa Nuhu ya dakatar dashi da fadin " No! Ita ce. Bari na fada maka gaskiya sonta kakeyi, you're deeply in love with her sosae, Ina fatan ka fahimci hakan?" " Yarinya ce bana tunanin tayi 15 yrs ma" Nuhu yayi dariya yace " Baka ji ba akace age is just a number ba! Ai ya mafi Dadi gidan ku daya, tana yarinya se ka kissima Mata sonka cikin zuciyar ta" Yaya yayi shiru yana ta aunawa a karshe yasan hakane so na yake Amma Yana hango how possible is it muyi aure? Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence to 09063467258 [15/12, 10:38] +227 98 36 59 34: 17 Kamar yadda Nuhu ya bashi shawara kawai ya fara yada propaganda din shi akaina, hakan yayi, ni kaina bazan iya ce muku ga yadda akai ba, kawai dai nasan na ganni tsumu tsumu a cikin soyayyar shi, bazan ce ga ta inda aka fara ba Dan Nima banyi aune ba se kawai jina nayi deeply in love with him. Da farko dai nasan ya tsiri Yi Mana lesson, duk lokacin da aka idar da sallar maghrib lokacin zai dakko past questions dinsa na neco da waec Wanda suke in a book form, zai Kira mu nida Siyama mu zauna muyi karatu, yawanci Siyama Bata da interest dukda ita din ce qualifying exams din ke gabatowa amma Babu wani hankali da take mayarwa duk iya kokarin kuwa da Yaya yakeyi Dan ganin tana fahimta. Ya bamu wani question ta maths ta 1994 muyi solving, na dage Ina ta cracking brain dina wajen ganin nayi solving Amma ita wani littafin hausa ne a hannunta ta saka cikin note book dinta me suna zazzafar kauna in jita da Fadi. Na Gama na dubeta Naga yadda take murmushi kamar bakinta zai yage nace " Siyama Wai ba Zaki zo muyi solving ba har se ya dawo" Ta ture hannuna daga littafin seda ta Kai karshen page din sannan ta dubeni tana murmushi tace " Ke rabu dani, bazan zauna nayi ta Bata lokaci na ba" Da mamaki na kalleta nace " Karatun ne Bata lokaci? Lallai Kam!" Tace " To meye amfanin shi, kina ganin dai Ina gamawa aure zaayi min meye abin damun kaina!" Nace " Ke Siyama! Ta Ina Kika sani?" Tayi dariya tace " To Mino aure zaayi Mata, Baki ga ranar an kawo Kaya gidannan ba, to kayan ta ne tana gamawa aure zaa mata. Barni nayi karatun soyayya ta ita zata fushe ni" Nayi Jim jikina duk yayi sanyi, Kar Nima suce aure zasuyi min idan na Gama Olevel dina, na girgiza Kai nace a raina ai bazai yiwu ba tunda dai ni ba Yar su bace. " Ni kuwa Kinga Ina son nayi karatu, saboda Abbuna yace Yana son yaga na Zama medical doctor, Allah sarki Allah ya jikanka Abbuna" Na fada Ina sunkuyar da kaina na maida hankalina Kan maths din Wai ko na samu abin ya fita a raina, but the pains is always there, kullum na tuna shi Ina jin kamar yau Ina zaune aka fitar da gawar shi a idona! Wannan karatun da muke shi yasa muka Kara shakuwa sosae dashi, na fara damuwa da alamuran shi, har idan ya fita na Kan tambaye shi Ina yaje ko Kuma idan ya wuni ban ganshi ba da zarar ya dawo Zan same shi na fara tuhumar shi inda yaje tun safe ban ganshi ba. Ummaan su duk hankalinta baya kanmu, ta tattara duka hankalin ta wajen shirye shiryen bikin Mino, Dan haka se Nima na Dan samu a bit of yanci a gidan. Wata ranar alhamis muna zaune Muna Hira dukkan mu, ranar har Baba, daya dawo daga port inda anan yake service saboda Yaya ya riga shi hada makaranta, ya zauna Banda fafa Babu abinda ke fita daga bakin shi, ni Kuma Ina gefe se kallon shi nake yadda yake zuba karya Dan yasan Wanda yake yiwa karyar ba su San ko Ina ba se ringim. Mikewa nayi na tafi na dakko books Dina nazo na zauna na fara karatu, ganin hakan yasa Yaya dawowa gefena ya zauna yace " Good girl! Gwara muyi karatu ko?" Na dago na kalle shi Ina sakar Masa murmushi tareda gyada kaina, yayi murmushi shima kasa kasa yadda ni daya zanji yace " I love your dimples!" Nayi saurin yin kasa da kaina Ina murmushi softly Amma bance komai ba, yayi Yar dariya da ta saka naji wasu knot na warewa a cikin cikina, " Kunya kike ji? You look really beautiful idan kina jin kunya" Na rufe fuskata na cuno baki nace " Kana hanani nayi karatu fa!" Yadda na shagwabe murya yasa ya shafa Kan shi sannan ya maida hankalin shi akan littafina Yana min bayani. Se muka ji sallamar Kawu Sa'idu, dukka muka Masa sannu da zuwa ya amsa sannan ya nufi dakin su, Ummaah dake bakin kofar ta bi Bayan shi. Ya zauna ya dubeta a kufule ita Kuma tambayar shi take dalilin da yasa ya dawo gida da wuri, muma duk a waje we were wondering dalilin dawowar shi da wuri. Bai amsa ta ba yace " Zinatu me ye wannan nake gani? Nufin ki duk yadda nake kokarin a banza kike so ya tashi" " Me ya faru Kuma?" " Tambayata ma kike? Ke wacce irin mace ce, kullum Ina waje Ina kokarin ganin rayuwar mu ta inganta Amma ke Ina tufka kina warware min" " Kaga ni fa ba gane abinda kake fada akai nake ba, ka fito kayi magana Sai zagaye zagaye kakeyi" " Au Baki gane ba? Me yasa Kika bar yarinyar can har take karatu, kinsan in har tayi karatu zata San kanta Kuma zata nemi ja dani, kinsan bazan iya samun komai akan dukiyar ta ba in har ta Yi karatu, to Dan me yasa Zaki barta take karatu?" Tayi tsaki Wanda yasa shi Kara harzukuwa yace " Ni zanyi magana kiyi min tsaki? Meye nufin ki" Itama cikin daga murya tace " Ya bazan maka tsaki ba, duk kokarin da nake ganin mun cimma burin mu Amma Kai baka gani?! Meye zaka dinga tsorata Bayan munyi da Kai aure zaa Mata da Wanda yafi kowa munin Hali a duniya, yadda ba zata taba fahimtar potentials dinta ba! Ka barta tayi ta karatu bazai taba Mata amfani ba, Bayan haka aure a shekara goma Sha biyar zaayi mata, Kai dai Yi kokari kaga ka samu yadda zakai ka juya zuciyar da tunanin Yan uwan ka!" Kawu ya sauke ajiyar zuciya, ya kalleta with adoration yace " Kina da kwakwalwa! Kinsan wannan satin dukka zasu zo saboda kamawar December, anan Zan samu na Gama kullin da ya kamata nayi!" Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment through 09063467258. [15/12, 10:38] +227 98 36 59 34: 18 Babu jimawa Dan ko sati baayi ba na fara exams dita, ana gamawa na daina zuwa, haka Ummaan su tace mu daina zuwa gwara mu zauna a more mu a gida. A wañnan lokacin Babu wani aiki na gida da ban iya ba,gaba daya na canja from the butter Afiyya to a house help, wanki ma da nake ganin wahalar shi shima na iya sosae Dan har nata take bani nayi Mata, ayyukan dake sani wahala duk na daina jin wahalar su tunda na riga na sawa Raina sun Zama dole, Dole se nayi Dan hakan Babu amfanin na dinga Bata Rai na a banza. Rayuwa sosae take canjawa Kuma indai Kai mutum ne dole ka karbi wannan canjin da yazo maka. Ranar da zaayi hutu ranar zamuje karbar result din mu Kuma a wañnan ranar Rooks tace min zasu taho daga NY, Dan hakan fuskata kawai zaka kalla kasan Ina cikin madaukakin farin ciki. Na Gama shiryawa na fito tana zaune kofar daki kamar yadda ya Zama kullum nan take zaune, tana bin gidan da kallo, ta kalleni tayi tsaki Wanda yasa na juyo fuskata dauke da murmushi, tace " Daina kallo na se kace mayya, da wasu kumatun ki a gurin masu lotsawa" Maimaikon naji haushi se na Kara sakin murmushi Wanda ya bayyanar da hakorana, ta mike zata kawo min duka nayi saurin gocewa tayi tsaki ni Kuma nayi saurin ficewa Ina dariya, Yaya na samu tsaye shi da Mino a kofar gida, idonta yayi ja da alamu kuka tayi, shi Kuma fuskar shi na nuna lallashi, ganin su a wañnan yanayin se naji Babu dadi ban Kuma tsaya ba kamar yadda nayi niyya, se Yaya yace min " Ba magana?" Na juyo Naga Mino na Mana wani kallo se na dauke kaina nace " I saw you guys talking shiyasa!" Ya harareni yace " Ke na zauna jira, Ina son muyi magana kafin ki tafi, shi ne kin fito zakiyi tafiyar ki?' Na tsaya tareda daidaita tsayuwa ta nace " Yaya! To gani ai" Ya matso gefena, we were so close da har Ina iya jiyo kamshin turaren shi me sanyi, kodan saboda idan naji kamshin Ina jin sanyi cikin Raina ne shiyasa nake jin sanyi ne dashi. Ya fara tambayata ko naci abinci? Saboda yasan ba lallai an bani ba, nayi murmushi Ina kallon shi nace " I ate, ka barni naje sauri nakeyi" For that mean time mun manta Mino na tsaye, ita Kuma se kallon mu take bakin ta a bude, tasan we're close Amma batayi tunanin closeness din mu yakai haka ba. Nayi gaba shima ya biyo bayana, haka muka jera Muna tafiya Yana ta min hira se Naga within shortest of time har mun karasa makaranta, lokacin an baje se kalilan dake zuwa karbar result din su, Ina karasawa class teacher din mu yace " Amina Baki zo da wuri ba" Na langwabar da kaina nace " Sir kayi hakuri" Ya gyada Kai na gaishe shi sannan Suka gaisa da Yaya, ya Mika masa result yace " Tayi kokari sosae na gaske kuwa, idan akwai abinda yafi na daya tabbas Amina zata dauka, she sure is an asset!" Nayi murmushi Ina jin dadin praises dinsa, Yaya ya Masa godiya sannan muka juyo, ya dubeni da idanun shi da Suka washe tas daga Jan da sukai dazun, sunyi haske har wani maiko maiko suke, he looks so happy Wanda yasa naji kamar banida wata damuwa se kallon fuskar shi da murmushi yaki daukewa akai! " I'm proud of you!" " Thank you" Se Kuma mukai shiru kawai muna tafiya a hankali, iska na kadawa kadan kadan duk zafin garin Ringim Babu Sabida sanyi ya fara shigowa se bishiyo Yi dake kadawa! A Haka muka karasa gida zuciyar mu tamkar an Mana bushara saboda kallon mu kawai zakayi kasan farin ciki na dawainiya damu. Tun daga nesa naga mutum ya juya baya, gabana ya yanke ya Fadi I can swear tamkar statue din Abbuna ne a tsaye, hatta tsayuwar jikin da komai tamkar na Abbuna, Yaya ya dubeni yace " Kinga Uncle Babawo! Let's go to him" Na dauke kaina na cigaba da tafiya ta a hankali tamkar kwai ya fashe min a ciki, Bai lura da yanayin da nake ciki ba ya karasa gurin da Uncle Babawo ke tsaye ya rike hannun sa, Ina hango tsantsar farin cikin da yake ciki na ganin kawun shi. Yana juyowa muka hada idanu dashi ya saki hannun Yaya ya nufo ni fuskar shi dauke da farin ciki, he looks so much like my Dad, se naji fushin da nike dashi bazan iya cigabawa ba, na nufe shi da gudu Amma Kuma se na kasa rungume shi na rike hannayensa and I found myself crying, yayi shiru yana bubbuga bayana Yana fadin " Ya Isa! Shiyasa tuntuni naki zuwa saboda banason na ganki kina kuka, ya Isa I'm sorry kinji?" Na gyada Kai na, na fara share hawayena se Kuma na fara dariya Ina gaishe shi, ya dinga kallona daga fuskata da ta canza sosae zuwa kayan dake jikina, ya dubi Yaya yace " Daga Ina kuke Haka?" Nayi sauri nace " Naje karbar result Dina ne, dama bansan wa Zan nunawa ba, class teacher din yace nayi kokari sosae" Ya gyada kan shi ya karba result din Yaya ya shige gida, he went through everything sannan ya shafa kaina yace " I'm proud of you my Baby. So bani labarin Ringim" Nayi shiru bansan me zance Masa ba, zance Masa abincin da zanci ma wahala yake min, ko Kuma Zan fada Masa tamkar Yar aiki haka nake a gidan riko na. Na girgiza Kai nace " Nasan yanzun kazo, idan ka huta I'll gist you" Ya gyada Kai na Mike na Masa sallama na bar shi da result din a hannu Yana kallona har na shiga gida, Ina shiga na samu ana gyaran kayan Miya, nasan saboda Baki yau zaayi Miya " Gidan uban wa Kika tsaya? Baki San kinada aiki a gida ba ko?" Naji muryar ta daga gefena, bance Mata komai ba nasan zuwa lokacin ta Saba da wannan halin nawa tunda akan shirun da nake Mata bazan iya irga sau nawa tana kaimin hannu jikina ba, Amma anjima idan ta Kara min irin haka ko kallon ta bazan Yi ba Amma Kuma Zan Yi abinda tace. Kamar lokacin se na shiga daki na cire uniform Dina nazo na daura shinkafa, kafin ta dahu an kawo markade, nayi Miya Ina jin kamshin na duka na, se naji yunwar da nake ta dannewa ta taso min, naji Yunwa nake ji Amma se na daure na koma daki har lokacin da zaa bani nawa. Mino na zaune Itada Siyama suna hirar bikin da dudduba Kaya, na kwanta Siyama tace min " Afiyya ke baayi Miki ankon ba? Ki fadawa Uncle Babawo tunda yazo" Nayi murmushi kawai bance Mata komai ba, to me zance atamfa falle biyu an kasa min bayan da dukiyata aie cin abinci. Bayan sallar laasar Ina cikin tuka tuwo naji sallama a bakin kofa, cikin sauri na Mike Dan Babu tantama muryar Rooks ce, tana ganina ta taho da gudu tana sakin ihu " Afeey darling!" Na rungume ta a jikina Ina fadin " Rooks darling welcome" Ta sakeni tana Kare min kallo na samo Mata kujera ta zauna gefena ni Kuma Ina tuka tuwo, ta kalleni tareda matsar da kujerar ta tace " Baki jin zafi? Bazan iya Zama anan ba" Ta tashi ta koma can nesa Dani, nayi murmushi Ina tuna da can lokacin da nake da gata ko suya ake a kitchen bana shiga Wai kada ya fallatso min, gani a gaban murhu Ina tuka tuwo. " Ya hanya? Ina Mummy?" Tayi murmushi tace min " Mummy da zamu taho tare se tayi bakuwa, matar yayar Abbah ce tazo wannan ta Istanbul din" Bansan ta ba Amma Ina jin ta a bakin Rooks, na gyada Kai muka fara Hira har na Gama kwasar tuwon, ta rkeni idanun ta sun kada tace " You do all this everyday?" Na langwabar da Kai nace " Yeah! And I'm fine our little secret darling" Na fada Ina Mata wink, ta biyo ni daki hannuna cikin nata, anan taga su Mino Suka Mata magana ta gaida su sannan tace min " Me yasa komai se kice it should be secret, you are suffering fa" Nayi dariya na dauki hijab na fito Dan tun safe Kawu Sa'idu yace idan Mummy tazo na tafi gidan ta. Na fito Ummaan su ta fito ta dubeni, wani skirt da riga ne a jikina ya dage saboda jikina ya fara karbar hormonal changes, atamfar tare Uncle Babawo yayi Mana da Rooks wani zuwa da yayi, Ash ce Kuma kunsan atamfa Ash nada saurin kodai so duk ta kode, " Ki wuce ki canja Kaya, ki saka na wannan akwatin naki" Na juya nace Mata " Ai duk kin daukar wa hafsa, saura kadan Zan saka da biki" Ta daka min tsawa Rooks tayi gasping saboda tsorata da tayi ta kalleni taga ki gezau banyi ba , na koma na dakko wata atamfar blue na saka na fito muka tafi. " Afeey Dan Allah haka kike rayuwa? Kingan yadda Kika koma kuwa? Nidai gaskiya Zan Fadi gaskiya" Na girgiza Mata kaina nace " Zan daina yadda dake, idan na fada me Zan canja Rooks? Bazai canza komai ba sede bacon rai, Nanny tace min watarana komai zai wuce and I also believe in that!" Hakan Dana fada se yasa tayi shiru kawai muka cigaba da tafiya har muka zo gida, a parlor mukaa samu wasu Yan samari suna zaune, tunda muka shiga hankalin su ya koma kaina, Rooks ta karasa tana fadin " Yaya nd Yaya shehu sannun ku da zuwa!" Suka amsa Mata, ta dubeni sannan ta dube su tace " My cousin Afiyya" Na gaishe su Suka amsa da murmushi a fuskar su, dayan ya gyara Zama Yana kallona da niyyar yimin magana se ya fitowar mummy da bakuwar ta ya katse mu " Abin kunya ai naku be da Baku San inda yarinya take ba, dangin uwa da aka sansu da jin Kai Amma ku kuka Yi fatali da yarinya marainiyar kwaya daya, abin kunya akanki ya Kare Mariya" Mummy ta fada tana huci " Nidai na fada Maryam, Kun kasa rike yarinya kwaya daya Kun barta tana watangaririya a Ringim, kunci amanar zumunci.." "Ku me kuka ci! Ke kin Isa ma kiyi zancen zumunci, kinada Baki? Ai Baki da bakin fadar wannan" Duka muka Yi shiru muna kallon su, ni ba maganar su nakeji ba se kallon matar da ke ta kumfar Baki nake, so nake na tuna fuskarta, why does she look so much like me? Babban Wanda shi ne Sarki ya karasa gefen mahaifiyar shi ya rike hannunta Yana fadin " Ummiey ku Bari Mana Dan Allah, mu tafi" Ta kwace hannunta tana fadin " Zaki San ni Kika fadawa magana Maryam" Mummy tayi tsaki tace " Kije da borin kunyar ki dai!" Ni ban taba ganin manya na fada ba, se Naga scene din banbarakwai, ta juya tana huci ko lura batayi Dani da nake tsaye ba, tana fita shehu ya bi bayanta, na zauna Ina gaida Mummy wadda lafiya kawai tace min tana kuka, Rooks ta dawo gefena ta zauna idanunta sunyi ja itama, waya ta dauka ta fara fadin " Babawo kazo ka sameni Ina gida, ku taho da Tijjani yanzunnan. Afiyya ta gama Zama gidan Sa'idu tunda shi Maci amana ne!" Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria. Send evidence of payment through 09063467258 [15/12, 10:38] +227 98 36 59 34: 20 Kamar yadda yayi min alkawarin cewar zai zo da yamma hakan ce ta faru,sede shi kafin yazo Yaya ya riga shi zuwa. Muna daki ni da Rooks ni Ina kwance Ina kallon frozen cikin system ita Kuma tana ta ciye ciye. Me aikin su ta kwankwaso sannan ta shigo tace Mana a parlor Yaya yazo. Nayi saurin mikewa Wanda yasa Rooks kallona tace " Meye abin sauri kamar Zaki Fadi?" Nayi murmushi nace " Ba Dadi jira" Ta tabe baki ta cigaba da tauna popcorn din da take ci, na zauna Ina yarda hijab din hannuna nace " Rooks naaa! Muje Mana" Ta kalleni tana murmushi tareda fadin " Ban taba ganin kina gaggawa akan Abu ba" Ban ce d ita komai ba na zura hijab dina na nufi kofar fita a bedroom din, tayi saurin mikewa ta biyo bayana, a parlor muka same shi an jera Masa drinks kamar wani bako, Mummy dama ta fita tun dazun ta Shiga fada, kamar yaji footsteps Dina ya juyo ya zuba min idanun shi , na Dan kalleshi briefly Ina murmushi sede idanun nashi bazan iya kalla na tsawon lokaci ba, Zama nayi har lokacin I felt his eyes akaina nace " Yaya tun jiya baka zo ba?" Ya danyi murmushi yace " Haba dama kina nemana ne?" Na tura bakina Wanda yasa shi dauke Kai ya maida Kan Rooks dake faman tambayar Ina yaje tunda tazo Bata ganshi ba. Nan muka hadu munata Hira wadda mostly ma shida Rooks dinne, se shi ne yake sako ni a ciki. Mun fi minti talatin se ga sallamar Yaya shehu, na daga idanuna Ina kallon shi, he looks so much like baban su Rooks, kana kallon shi ba se an fada ba kasan he's a royalty, tafiyar shi ma kawai cikeda Isa yake yinta, a fuska zakaga tamkar Yana da girman Kai Amma idan ka zauna dashi zakaga ko kadan he's simple as what you can't imagine, kyakyawa ne musamman idanun shi Dan ni dai su suka fi burgeni dashi, se Kuma leben shi. Kullum idan Yana magana lips dinsa kawai nake kallo yadda yake motsa su a hankali. Yana da tsawo kana kallon shi zakasan Yana zuwa gym yadda abs dinsa ke fitowa musamman idan kayan jikin shi sun Kama shi, he's a man to kowanne gaba. Muna hada idanu ya sakar min murmushi, na mayar masa har ya zauna ya bawa Yaya hannu suka gaisa, Rooks tace " Ya shehu wannan sunan shi Yaya, gidan su Afiyya yake Kuma cousin dinmu ne" Ya Shehu ya saki fuska ya Kara Mika Masa hannu a Karo na biyu suka gaisa, Rooks ta dubi Yaya tace " Yaya Shehu, Afeeys' cousin and also my cousin!" Yaya ya tsira Masa idanu kamar zai ce wani Abu kawai se ya Mike, Ina ganin hakan Nima na tashi Ina fadin " Yaya tafiya zakai?" Ya gyada min Kai yace " Ai Naga kunyi bako, Zan dawo anjima" Banji dadi ba Sabida ganin shi ma ko bazan Yi magana ba nutsuwa yake saukar min, Haka Ina kallo ya tafi na dawo na zauna Ina duban Ya Shehu da yake kallona admiringly yace " Afeey Babu magana! Ko na tafi I'm not welcome?" Na girgiza Kai na zauna na gaida shi, ya Bata fuska yace " Seda ma na roka" Na danyi shiru Ina kyabe fuskata kamar zanyi kuka, yayi dariya wadda tasa na shagala Ina kallon shi yace " I got you exactly where I wanted to! Wasa nake come on bani labari" Nima se nayi dariya na gyara zamana nace Masa ni banida labari, se yace min zai bani Mai dadi, Rooks dake gefe tace " A'a ya kamar Kun manta Dani ne?" Ya kalleta Yana harar ta da Wasa yace " Shut up my Friend! Tashi anan" Haka ta Mike Ina Mata dariya tace Masa ita tafi son Sarki tasan da shi ne bazai taba korar ta ba not ever, yace yaji taje, abinda na lura dashi they're close gaskiya sun Kuma Saba sosae. Tunda ta tafi se mukai shiru se shi yace " Ok tell me, me yasa Baki taba Neman Ummiey ba" Se na kalleshi sannan na dauke kaina daga kanshi nace " Ta Yaya Zan nema ta bayan ban santa ba!" " Hakane Kuma! I hope kin yafe musu?" Nayi dariya nace " Basuyi min komai ba fa! Stop making it sounds somehow" Ya gyada Kai. Kwanaki suka cigaba da tafiya kullum Yaya Shehu se yazo Haka Yaya sede Basu Kara haduwa ba, idan Yaya yazo se yayi ta complain shi baya son yawan cousins gaskiya, ranar har na Dan ji haushi nace Masa ko baya son na shirya da dangin Mama ta ne, se ya fara kame kame shi ba Haka yake nufi ba kawai dai shi tsoro yake ji, banma tambaye shi tsoron me yake ba saboda hankalina baya gurin, Yana tunanin dalilin da yasa har yanzun Ummin su Bata neme ni ba. Da daddare na samu Mummy a daki ana gobe zaa fara bikin Mino, tana ta ware Mana kayan da zamu saka na biki na shigo da sallama, ta aje rigar hannun ta tace " Afiyya ya akai? Kinci abinci?" Na gyada Kai na sannan na zauna Dan nesa da ita nace " Mhmm Mummy...mhm" " Menene? Fada min" Nayi kasa da kaina Ina Wasa da fingers Dina nace " Mummy Ina son naje gurin Ummin su Yaya Shehu" Ta Dan kalleni for some seconds sannan tace " Ki Kira Rooks ta raka ki" Wani dadi naji a raina Amma har na tashi Zan tafi se na dawo nace " Mummy Amma bakiji haushi ba ko?" Ta kalleni ta sakar min murmushi tace " Banji haushi ba, you need to meet her tuntuni. A gaida su" Tana zaune Kan makeken gadon ta , tayi kwalliyya cikin doguwar riga ta lace, fuskarta Babu kwalliyya Amma tayi ado da jewelry set masu tsada da daukar hankali. Hannunta da kafarta yasha kunshi Banda kamshi Babu abinda ke tashi, gefenta sarki ne se Shehu dake zaune akan bed table. " Ummiey wannan fa ba dalili bane gaskiya, saboda Kuna fushi da babanta se ku sauke akanta? Haba Ummiey ke me zumunci ce fa wallahi kunyar yarinyar nakeji, idan Kika zauna da ita she's so much in pain". Ta kalleshi sannan ta maida kanta Kan tab din dake hannunta yace " Kenan ganging kukai kunzo kuyi min fada?" Shehu yayi saurin dariya Yana daga hannu, yayinda sarki yace " No Ummiey ba Haka bane ba,kawai munji ya kamata mu fada ne" Tace " Naji! Dakko min veil Dina ku rakani na ganta" Shehu yayi saurin mikewa Yana fadin " Ko kefa Ummiey!" Tayi murmushin jin Dadi, sede kafin ya fita Nadia ta shigo tana fadin " Ummiey ga Afiyya tazo" Tayi saurin mikewa jikinta har Dan rawa yake tace " Da gaske?" Bata jira amsar su ba tayi waje, Shehu ya dubi Sarki yace " She longs for her Amma saboda dlili marar tushe tana punishing kanta" Sarki yayi murmushi ya dafa kafadar Shehu Suka fito parlon. Ina tsaye Harith na ta cemin sufa sunyi fushi dani, se gata ta fito. Rooks ta Kama hannuna muka karasa ciki, fuskarta da dariya ta bude min hannayenta, Babu musu na shige jikinta ta rungume ni, Yan kwanakin kam they were one of the happiest days of my life! Bayan ta sakeni na gaishe ta tana ta kallona tana fadin mamakin girman da nayi takeyi, time sure flies! Duk yadda take Jana da Hira se na kasa sakin jikina se hirar ta koma tsakanin ta da Rooks, seda Yaya Shehu yazo sannan na saki jiki mukai ta hira dashi, se bayan Sha daya na dare aka raka mu gida. Daga nan aka fara bikin Mino, anyi biki Babu laifi sede son barka, kwana biyu aka daura aure da dare yayi aka kaita gidan ta anan Sabin fegi. " Maryam ya akai?" Kawu Sa'idu ya tambayi Mummy lokacin da suka hadu duka suka je gidan, Bayan an nutsa da bikin. Ta dago ta kalleshi cikin idanu kamar yadda yake kallonta shima cikin idanu, gaba daya se taji ta duburburce ta fara stammering, uncle Babawo yace " Yaya Sa'idu dama zamu ce ne zata tafi da Afiyya can NY!" Ya Kara dago idanu ya kalli Uncle Babawo yace " A'a! anan zata zauna" Gaba daya suka hada Baki duka su ukun sukace to! Ya Mike ya fice ya barsu zaune tamkar ruwa ya cinye su, Mummy tayi zumbur ta mike tare da Dora hannunta akai tace " Me ya faru? Menene wannan?" AFIYYA is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment to 09063467258 [15/12, 10:38] +227 98 36 59 34: Muka zauna mukai jugum jugum mussaman ni da nake ganin ni ce na Zama silar fadan uncles dina, se lokacin na fahimci maganganun da Mummy da wannan matar suka dinga exchanging, wato tazo tana Mata fadan sun kasa rike ni kenan? To idan haka me wannan matar ita ce Yar uwar mamata da akai auren su tare, na Kara zurfafa tunanin da nake nace tabbas biri yayi Kama da mutum, no wonder yaranta ke kallona kamar alien, Nima Kuma nake kallonta tamkar an cira fuskar ta an saka min, shiyasa Mummy ke ce Mata sune Suka ci amanar zumunci kenan! Ina wannan tunanin naji sallamar Kawu Tijjani da Uncle Babawo, shi banma San da zuwan shi ba Kuma dama tun asali shi dinne nafi Jin haushin shi, saboda Ina ganin shi yafi kowa kusa da inda nake Amma bai taba zuwa yaga inda nake ba. Ganin Mummy a zaune ta hade Kai da gwiwa tana ta kuka yasa duka sukai kanta Basu ma kula da gaisuwar da muke musu ba, na Mike tsaye na Kama hannun Rooks muka tafi kitchen " Me ya faru Anty Maryam wallahi kin tayar min da hankali" " Ta Yaya bazan tayar maka da hanakli ba Tijjani? Kai da Zan tafi bayan rasuwar Yaya me nace maka? you should be checking on Afiyya lokaci zuwa lokaci, Amma me? Kayi, bakayi ba, Kai da zaka saka idanu akan yadda take rayuwa baka masan wanne Hali take ba balle mu da muke wata uwa duniya! Ta Ina zamu sani?" Uncle da yayi shiru yana sauraron ta yace " Mom Rooks! Duk tone tone bashida amfani kowa yayi laifi a cikin mu, bamuyi zunmunci ba Amma yanzun ba lokacin wannan bane ba, kawai let's decide ya zaayi da Afiyya?" " Ni Zan tafi da ita wannan Karan Bai Isa ya hanani ba, yasa anzo har gida an gaggaya min magana, Dan hakan Zan wuce da ita ta koma hannuna" Kawu Tijjani da se lokacin yayi magana yace " Mom Rooks kiyi hakuri nasan I've failed you, tabbas banyi abinda Kika cemin ba Amma Kuma akwai abinda na kasa fahimta, ni bansan yaushe Yaya Sa'idu ya Zama abin tsoro ba, nazo Ringim say da yawa na Kuma San halin da Afiyya take ciki Amma idan na sameshi zanyi Masa magana se na kasa...." " Shirme kenan! Waye shi Sa'idun? Bai Isa ba wallahi yayi kadan daga yau Babawo kada ka sake tura Masa kudi, idan ya ga dama kada ya ciyar da ita, you've been sending kudin makaranta, baka taba inquiring makarantar whether Afiyya tana zuwa ko Bata zuwa, ka dinga tura mishi kudi yarinya ko abinci say uku ba taci. Ka bani kunya! Duk Ina plans dinka?" Sudai hakuri suka bata, har ta sassauta, Muna daga kitchen Ina jin komai da suke fada, Mummy ma nada laifi ya kamata ta dinga Kira tana jin yadda nake Amma shiru itama sede tabbas laifin su yafi nata yawa a nawa ganin kenan. Rooks ta dakko juice daga cikin fridge ta zuba min cikin glass cup ta aje min, itama ta tsiyayawa kanta tace " Ina fata Mummy zatayi nasara mu tafi dake" Nayi murmushi bance komai ba, Haka kurum jikina ke fada min kada na saka Rai da yawa akwai sauran lokaci. Daga nan se maganar ta lafa, na cigaba da harkokina gidan su Rooks, da daddare Abban ta ya dawo yayi murnar ganina, seda suka kebe da Mummy yake ce Mata " Afiyya kamar ba ita ba, da farko fa ban gane ta ba" Mummy sarkin kuka se ta fara matse hawaye ta fara fada Masa duk abinda ya faru tsakanin ta da Ummin Istanbul, seda ta gama yace " To kiyi hakuri, tun farko Dana Bai dace ku barta anan ba gaskiya, I'm sorry to say Sa'idu ko gamawa yaranshi baiyi ba balle yayi shouldering needs din Dan wani. Se a kiyaye gaba, ita Kuma Hajiya Mariya kada ki Kara kulata har ta Bata Miki rai, kawai kiyi abinda ya dace." Washegari da wurwuri kamar yadda na Saba tashi na fito, gidan yayi shiru kowa na bacci na dakko tsintsiya na fara shara dukda Babu koami a parlon se Dan kura, akwai lokutan da nake ayyanawa idan har na bar gidan Kawu Sa'idu ko tsintsaiya ba Zan Kara kalla ba, Amma jikina is groomed da hakan yanzun da na kwanta nayi bacci sosae se naji jikina ciwo yake min, in no time na Gama gyara gidan nayi wanka na dakko sabon kayan da Mummy ta bani tun jiya nasa a jikina. Na saka hula na zauna nayi shiru Ina tunanin yau da gobe, a raina Ina adduar Allah ya zaba min mafi alkhairi, Zan iya binsu su Rooks din idan akwai kaddarar se na Sha wuya shima gidan su bazan ji Dadi ba, Allah shi kadai yasan me ya tsara min a rayuwata, Dan haka komai yazo min Zan karba. Sosae Mummy tayi mamakin gyaran da nayi, ta kalla Rooks tace " Ba abinda Kika iya malalaciya" Abban ta yayi dariya yace " Itama ba Haka aka so ba" Ta kalle shi tareda fadin " Wallahi kua! Allah sarki Yaya Allah ya jikan shi!" Muka amsa Amin sannan muka bita kitchen Dan yin breakfast, Muna gamawa muka hadu muka ci, na kalla table din dukda munyi girki Amma seda aka kawo daga fada, na dauki mug na hada tea me kauri na fara sha, Mummy ta zuba min wajen dishes uku cikin plate dina, tace " Ki cinye tas ko zaa samu ki Dan murmure, ramar nan tayi yawa" Haka mukaci Amma ko rabi kasa ci nayi saboda cikina yanzun ya Saba a bashi abinci kadan, ni na fara dawowa parlor na zauna Ina kallon wani movie, sallamar Yaya Sarki da Yaya Shehu tasa na maida dubana kansu, suka shigo Basu zauna parlon ba Suka nufi dining sukai joining dinsu, seda suka Gama sannan Suka sakko duka Suka fara Hira, ni bama hi nake ba hankalina Yana kan tab din Mummy dake hannuna Ina surfing internet. Shehu ya dubi Mummy ya matsa gefen ta yace " Mummy wacece wannan?" Ta dubeni sannan ta dubi sarki dake kallon ta with so much curiosity tace " Ki tambayi baban ku" Sarki ya matsa gefen Abban Rooks ya maimaita Masa tambayar da Shehu yayi, a take ya aje wayar shi yace " Kun tuna Anty dinku ta Lagos, sister Ummin ku?" Shehu yace " Of course! Anty Halima ba! Allah ya jikanta, Taya zamu manta ta. Ina yawan tambayar Ummiey Ina babyn data bari, se tace wai tana Nigeria!" Abbah ya gyada Kai yace " She's the Baby! Afiyya is your cousin" Duka Suka kalloni, intense din kallon yasa na dago se Naga sun sakar min Murmushi, na danyi yake kadan Zan maida kaina kan tab din Mummy ta dakatar dani, ita tayi min bayanin su, nayi murmushi bance komai ba saboda banida abinda zance din. Shehu ya dauki waya ya fita, Sarki Kuma shi ne bashida magana sosae Dan haka duka mukai shiru, Abbah da Mummy sun koma daki, Ina Rooks na tayi Masa hira muakji sallamar Harith da Nadia suna bin bayan Shehu, Ashe zuwa yayi ya kirasu. Naji dadi sosae it was like a mini reunion. Wajen azahar zasu tafi Yaya Sarki yace min nazo muje na gaida Ummin su, har na Mike Zan bisu se nace da Rooks Bari na gayawa Mummy, Ina fada Mata ta hade Rai tace " A'a kiyi zamanki, fita zamuyi" Cikin rashin jin dadi na fito I wanted meeting her, ko mutum daya da Zan nuna nace Dan uwan mamata ne, Amma nasan Mummy nada nata dalilin. Ina kallo Suka tafi Rooks ta bisu zata he gaida kakarsu a fada. Yaya Shehu dake tsaye gefena yace min " Zan zo da yamma, Zaki bani labari kinji?" Na gyada kaina, Nadia ta Dan rungume ni Suka tafi abinsu. Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 First bank of Nigeria Aisha Hassan kwalam, send evidence of payment to 09063467258 [15/12, 10:38] +227 98 36 59 34: 22 " Mom Rooks, Anty Mariya karku manta kokarin karbar Afiyya daga hannun Yaya Sa'idu ma ya gagare mu, balle mu kawo zancen auren ta. Ya kamata kowannne Abu muyi solving din shi one at a time. Amma bamu Gama fita daga wani ba kada mu saka kanmu a cikin wani." Uncle Babawo ya fada cikin nutsuwa, dukka suka Yi shiru Dan sure he has made a point, Amma Kuma dukda haka suna bukatar abinda zai kubutar damu. " Yanzun haka yarinyar zata cigaba da Zama a hannun shi kenan" Ummiey ta dubi Shehu da yayi kalar tausayi tace " Oya tashi ka fita, manya na magana kana saka musu Baki, bansan Ina kabar manners dinka ba" Ya mike sumsum ya nufi karamin parlon da muke ciki, kana kallona kasan I was not ok! Gefena ya zauna Yana kirkiro murmushi yace " Haeee! Tunanin me kike Yi?" Na girgiza Kai bayna nayi firgigit nace " Nothing!" Ya Dan tsira min idanu sannan yace " Afeey wani ya taba ce Miki Yana son ki?" Na kalleshi da sauri Ina zaro idanuna waje, na kalli gefena yasan Rooks nake nema, ya danyi murmushi yace " Tana daki ni dake ne kawai, nasan you're too young for love words Amma Ina ganin su kadai zasui saving din ki da wannan rayuwar da kike ciki.." Bai Gama ba nace " Anan Zan cigaba da Zama ko? Kawu Bai yarda ba ko?" Ya girgiza Kai yace " No...!" Nayi saurin katse shi Ina Murmushin takaici nace " You don't have to lie, nasan Bai yarda ba, dama bana expecting ya yarda, wannan itace rayuwar da Allah ya tsara min" Yayi shiru yana sauraro na, idanun shi sun tashi da asalin milky color dinsu Dan dama idanun shi ba fararare bane irin nawa, sunyi ja Amma ba jajawur ba, I can see tsagoran tausayina a ciki, he looks helpless yace " I'm sorry!" Na Mike tsaye saboda Ina jin gurin yayi min zafi I'm suffocating, na kalleshi nace " Why? Bakai min komai ba, karka manta ance duk abinda yazowa bawa ya karba, nasan watarana I'll be happy, nasan watarana komai zai Kare, kilan sede labari. I've to live tunda haka Allah ya kaddara min." " AFIYYA I love you!" Zan iya rantsewa cewa hatta dogon hannun dake jikin agogo wato second hand ya daina juyawa, tamkar lokaci ya tsaya Haka na gani, komai ya tsaya cak se bugun zuciyata kawai da ya karu, idanun shi cikin nawa, wasu molecules ke fita a nashi suna Shiga cikin nawa, a wañnan shekarun I couldn't comprehend abinda nakeji, se de da muka cigaba yiwa juna kallon kurilla se naji tamkar jiri zai daukeni, cikin sauri nayi shutting idanuna tareda Jan dogon numfashi na koma sofar Dana tashi na zauna jagwab! Nafi mintina biyar kafin a hankali na bude idanuna sede ni daya ce a zaune a parlon, shi din baya nan. Cikin sauri na Mike na bude kofar da zata hada ka da main parlor Amma Babu kowa cikin parlon, na lumshe idanuna na koma parlon na zauna, Rooks ta shigo tana cemin naje Mummy tana Kirana, na Mike tamkar wadda kwai ya fashewa a ciki na sameta a bedroom dinta. Na zauna gefenta kamar yadda ta nuna min, ta Jima tana min tambayoyi akan makaranta da Kuma yanayin zaman da nake gidan Kawu Sa'idu, Amma mirsisi na ki fada Mata, a ganina Babu wani amfani da zaiyi, tunda dai komawa gidan ya zame min dole se nayi, tace " Kiyi hakuri da duk yadda rayuwa take zuwa Miki, Allah shi yasan me yake nufi da faruwar hakan, saboda wasu dalilai min Bari ki zauna anan ki karasa makaranta, Kinga na Miki alkawari da kin Gama secondary Zan tafi dake. Kinji?" Nayi Dan murmushi da zai karfafa Mata gwiwa nace " Allah ya kaimu Mummy nagode!" Ina Gama fadar hakan na sauka na fita daga dakin nayi bayan gidan na tsaya, na tsugunna na Kara tashi wani irin abu nake ji cikin zuciyata, Banda tafasa Babu abinda takeyi, na lumshe idanuna da na tabbatar sun kada sunyi ja, jinsu nake har zafi suke min saboda bacin Rai, na Kara tsugunna wa nasa kaina tsakanin cinyoyi na na fara kuka a hankali, na Jima inayi seda naji zuciyata ta Dan rage radadin da take min sannan na wanke fuska na koma daki, Rooks na samu idanunta sunyi jawur tana hada Kaya, na zauna nace " Me ya samu fuskar ki?" Tana jin abinda nace se ta fara kuka, na tsaya Ina kallonta Ina ayyana me yasa zatayi kuka da uwarta, da ubanta, cikin gata da kwanciyar hankali kukan me zatayi ita kuwa? " Wai anan Zaki zauna, Wai ba zamu tafi dake ba" Naja tsaki nace " Shi ne kike kuka? Allah ya kyauta" Ina fadar hakan na wuce toilet saboda wata kwalla ke son zubo min daga idanuna. Wani Abu da Suka manta Babu Wanda yayi tunanin ya gudu Dani, na kanyi tunanin me yasa Suka dinga bin Kan Kawu Sa'idu Basu daukeni min tafi ba. Duk lokacin da wannan tunanin yazo min se zuciyata tace saboda haka Allah ya tsara. Kwana biyu da suka zo gaba daya bana cikin dadin Rai, gani nan gani nan dai, ana uku mukaje Mummy ta duba kayana, ta samu duk an kwashe haka ta loda min wasu, komai seda ta siya min sabo hatta panties, ta bani kudi me yawa tace na boye, tana tsaye na boye sannan ta siya min sabuwar katifa da tafi tawa girma. Washegari ta dawo dani Akan a Daren zasu tafi Kano zasu bi jirgi zuwa Abuja zuwa NY, a wañnan Daren nayi kuka kamar Zan cire idanuna, bana tunanin bacci kodan bacci barawo ne nasan ya dauke ni na farka. Da safe Dana tashi na kalli tsakar gidan hawaye ya kara gangaro min, na dauke su day hannuna nayi alwala nayi sallah sannan na fito ko komawa banyi ba na fara aikin Dana saba. Haka rayuwa ta cigaba da tafiya. A wañnan kwanakin shakuwa me karfi ta Kara Shiga tsakanina da Yaya, se na manta da abinda Yaya Shehu yace min Wanda tunda akai abin kullum kwakwalwa ta na tariyo min abin, idanuna na hasko min idanun shi, duk lokacin Dana tuna hakan se nayi gasping kadan, wani irin nishadi nake tsintar kaina a ciki. Haka kunnuwa na Basu gazawa wajen echoing wannan L word din daya furta. Amma influence din Yaya seda yasa gaba daya abin ya daina tasiri cikin Raina da zuciyata, saboda shi se na daina jin wahalar zaman gidan su, saboda shi nayi ta tolerating abubuwan da Zan iya maganin su. Ummiey da suka dawo Kaya ta kawo min sosae sannan tazo ta ganni ta bini da nasihu, ana gobe zasu tafi Istanbul na dawo daga islamiyyar da Mummy ta sani a marakawa, Yaya Shehu zaune yayi kyau cikin carton brown shadda, dinkin kanshi abin kallo ne, idanun shi masu kaifi na kaina dukda Yana sanye da farin glasses Wanda nafi tunanin medical glasses ne, Dan kusan ko da yaushe Yana fuskar shi, kanshi yasa hula wadda ta kafu kasancewar Yana Tara gashi, a hankali se naji yanayin nan ya fara dawowa, na dinga daga kafata a hankali har na Isa inda yake nace " Yaya! Ina wuni" Ya bini kallo, inaga Yana mamakin yadda na koma ne tamkar an zuke ni yace " Me yake damun ki? Kingan ki kuwa?" Nayi Dan murmushi nace " Nothing a Little stress" Ya harareni yace " Ban yarda ba, see Zan iya Kai karar kawun ki nan wajen human right fa" Se ya bani dariya dukda he's serious nace " Human right? Time ne" Se ya gyada Kai kawai ya fara tambayata yadda nake na Dan Jima a tsaye sannan ya Miko min Leda yace " I'll miss you so much, tunda like zuwa Nigeria Bata taba min dadin da tayi min irin wannan ba. I've found and uncut gem here" Na bishi da kallo Ina jin yadda words dinsa ke sinking a hankali ya dage min gira yace " Take care of yourself, ki tuna Ina sonki da lokaci yayi Zan aureki Inshaaa Allah" Na tura Baki nace " Wanne irin aure Kuma? Kai Yaya" Yayi dariya tareda sunkuyar da Kai yace " I'm serious ba lallai karamin kanki ya gane ba, just know someone somewhere loves you alot!!" Wannan kalaman nashi were deeply buried in my heart, Yaya seda ya saka na binne su saboda yadda ya dinga showering Dina da tashi kalar soyayyar. Dukda Bai furta ba Amma ni Kam zuciyata dumu dumu ta kamu da son shi, lokaci lokaci takan tuna Yaya Shehu Amma na yarda Zama wake daya is very toxic, wannan dalilin yasa Yaya Shehu baiyi tasiri cikin zuciyata ba! Duk wannan bidirin iyayen shi Basu sani ba sun tafi bin bokaye yadda zasu karba dukiyar hannun Uncle Babawo Amma Abu ya faskara, ko address din guraren ba su sani ba, se takurar da ake min ta Kara yawaita, Amma idan na fito Naga dansu se naji Babu komai watarana zai wuce. A hakan na Gama ss2 inada shekara Sha hudu, ni kaina na kasa lissafa yadda akai a 14y har nake ss2. Bikin Siyama ya tashi Amma bansan yadda akai ba kamar an binne maganar se ta mutu, tayi kuka kamar zata mutu, nasha jinta cikin dare tana fadin ita guduwa zatayi, ban taba tambayar ta abinda yake faruwa ba. Junaidu 10years leap! Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment through 09063467258 [15/12, 10:38] +227 98 36 59 34: 21 Ita kadai take ta kallon gurin da Kawu Sa'idu ya tashi tana Kuma tantamar ko tana cikin hayyacinta da har ta kasa magana dashi, ita dai Mummy Abu daya ta sani tunda Suka hada idanu da Kawu Sa'idu taji tamkar an Mata format ne cikin kanta, taji gaba daya tsoron shi ya kamata Wanda tunda take Bata taba ji ba, kasancewar yayi rashin ji Yana yaro Kuma shi kadai ne bashi da madogara a gidan yasa Suka Raina shi, Dan ita se ta ga dama take ce Masa Yaya, lokuta da dama idan kowa ya kasa fada Masa laifin sa to ita ke tunkarar shi ta fada Masa, dalilin da yasa basa shiri ko kadan gasu Kuma sako da sako. " Mom Rooks seda na fada Miki Yaya Sa'idu..." " Me ka fada min Tijjani? How do you want me to believe ni dinnan na kasa karbar Afiyya a hannun shi? Dan Allah Bari mana! Me Sa'idu yayi da na kasa fuskantar shi nayi maganaI'm a failure kenan" Uncle Babawo ya mike ya riko hannun Mummy cikin lallashi shi kanshi he's confuse sosae da sosae, shima when it comes to him baya tsoro dama Tijjani ne me tsoro, shi kuma Abbuna Yana da dauke kai, mutum ne me kawaici shiyasa tafiyar su tayi nisa shida Kawu Sa'idu. " Mom Rooks ki daina daga murya, tabbas something is fishy kizo muje mu hada Kai muyi tunanin possible solution" Mummy na dawowa ta wuce mu a zaune a parlor Muna game din whot, ko sannun da muke Mata Bata amsa mu ba, se naji jikina yayi matukar sanyi naji na daina gane su star, carpet, pick 2, general pick and stuffs. Na aje na hannuna tareda ja da baya na jingina kaina da jikin sofa, Rooks ta dubeni tace " Menene?" Na girgiza Mata Kai, ta bude baki da niyyar yimin magana taji Mummy na kwala Mata Kira, Haka ta mike ta tafi Babu jimawa ta dawo fuskarta kawai na kalla Naga Bata cikin jin Dadi,whot din ta tattare ta aje gefe tace min " Mu tafi daki" Na mike nayi gaba tabi bayana, wani iri nake ji na dinga jin kamar nabi Mummy daki na tambaye ta me ya faru? Ya sukai itada Kawu Sa'idu Amma se naki kawai na hakura, idan nabi a hankali zanji me akace, tunda a kaina ne na tabbatar. " Kina ganin kukan da kikeyi shi zai samo Miki mafita kenan?" " Darling ya zanyi? Na kasa tunanin yadda zanyi fa, ko magana kwakwara na kasa Yi a gaban shi" Abban Rooks ya ruko hannun ta cikin sigar lallashi yace " Allah ya kaddara zaman ta Bai Kare anan ba se kiyi hakuri kawai, Allah ya San me yake nufi" Bangaren Ummiey sunata Shirin tafiya maiduguri Dan suyi sati daya sannan se su dawo Ringim su Kara sati sannan su wuce Istanbul. Gaba daya Ummiey ta hautsuna gidan Kai ka rantse da koami na gidan zata tafi maiduguri din, Daddy na zaune shi da Shehu suna kallo ta fito rike da wayatta a hannu, " Wato Kai kowa Yana aiki Kai shi ne kazo ka tasa TV a gaba kenan?" Shehu ya kalli Daddy, Daddy ya kalle shi, ya Masa alamar ya tashi, Babu musu ya Mike yace " Ummiey yanzun me ya rage?" " Ko sannu ba zaka dinga leko ni kana min ba? " Ya sauke ajiyar zuciya yace " Kiyi hakuri Ummiey sannu da aiki, is there any thing I can help with?" Ta girgiza Kai tace " Yi zamanka kafin Baban ku yace bullying dinka nake" Daddy yayi dariya yace " Ummiey indai tafiya ta tashi ba Zaki zauna ki huta ba" Nadia ta karaso ta zauna kana kallonta zakaga so much stress a tattare da ita, ta kalli Daddy zatayi magana Ummiey tace " Kin hada boxes din guri guda, bana son mantuwa fa" Shehu dake tsaye ya saki dariya, Nadia ta tura Baki tace " Na hada komai fa Ummiey" Shehu ya zauna Yana kallon iyayenshi yace " Ummiey can I share my opinion here?" Ta gyara zaman ta tace " Why not? Me ya faru?" Yace " Ummiey tunda zamu tafi gobe, me zai hana mu tafi da Afeey Kinga it's an opportunity tayi reconciling da Yan can." Tayi shiru tana kamar tunani yayinda Daddy dasu Nadia Suma suke kallonta suna sauraron amsar ta, ta Dan kalli Daddy sannan ta maida kallon ta Kan Shehu tace " Tunanin hakan Bai ma zo min ba, Nads jeki kawo min wayata a bedroom na Kira Maryam" Daddy ya girgiza Kai yace " Not Maryam, Afiyya hannun Sa'idu take so shi ya kamata kije ki tambaya" Ta gyada Kai ta dubi Harith da shigowar shi kenan tace ya fita da mota zasu je gidan Kawu, Daddy ya dubi Shehu yace " Kaji Ummin ku fa tafiyar da zata iyayi a kafa shi ne har se taje a mota" Ta harari Daddy, Shehu ya daga hannun shi yace " Daddy ni dai ba ruwana!" Sukai dariya daga haka ta fita, cikin saa Suka same shi a gida, tunda yaji zancen zuwanta yasan Yana da nasaba Dani Dan hakan ya Zama cikin shiri, a tsakar gida aka shimfida Mata tabarma ta zauan, dama Harith Bai shigo ba a mota ya zauna. Suka gaisa sama sama ita da Ummaan su, sannan Kawu Sa'idu ya zauna Suka gaisa cikin mutunci, ta dago tana kallon shi kawai suna hada idanu se taji ta kasa magana ganin yadda ta Dan rikice yasa ya Kara rike idanun ta cikin nashi, " Hajiya Mariya akwai wani abunne? Ai yarinyar na gidan Maryam se zasu koma zata dawo nan" Ta mike tana fadin " Ai bansani ba, Bari naje gidan kawai" Tayi sauri ta juya har ta kusa zaure yace " Kada ki dauki yarinyar nan kije da ita wani guri" Ummiey ta juyo a hankali bakinta na San fadin abubuwa Amma suna hada idanu tace " Ina zan kaita kawai ganinta nazo Yi!" Ya gyada Kai Ummiey ta tafi tana jin jiri kamar zai kwashe ta, Ummaan su ta fara dariya tana fadin " Wannan Abu yayi , da bakai Haka ba da tuni komai ya rushe!" Shima dariya yayi yace " Gashi Ina juya su yadda nake so, da farko banyi tunanin aikin zai ci har haka ba, saboda malamin Yana tantanmar yiwuwar aikin akan Maryam da Mariya da Babawo, se gashi Kuma yayi" Ummaan su cikeda farin ciki tace " Yanzun tunda ka samu wannan se zancen karbar dukiyar ya kamata ka maida hankalin ka akai" Ya shafa Kai yace " Da kyar na karbi wasu filaye anan hannun Tijjani, Amma na gurin Babawo se anyi da gaske. Amma akwai wani malami a Niger an fada min naje gurin shi" " Ya kamata dai ! Da zafi zafi ake bugun karfe" Ummiey na shiga mota ta dafe kanta dan ji take kamar zai fado, Harith ya dubeta a tsorace yace " Ummiey what's wrong? Me ya sameki?" Cikin rawar murya tace " Kaini gidan kawun ka Bashir" Haka ya juya motar Suka nufa gidan su Rooks, dukkan mu Muna zaune mun samu bakuncin Shehu da Kuma Uncle Babawo, kamar ranar Suka fara haduwa se Hira suke duk yawanci akan diaspora ne. Shigowar Ummiey yasa Shehu mikewa da sauri ya nufe ta, ya riko hannun ta Yana tambayar Harith abinda ya faru, Muna kitchen muka fito, Mummy ta karasa ta zaunar da Ummiey ta fara tambayar ta abinda ya faru. Ta dubeni ta saki hannunta daga kanta tace muje daki zasuyi magana , Haka muka juya jiki a sanyaye, Ummiey tace " Maryam kin tabbatar Sa'idu baya bin bokaye?" Mummy ta kalleta da mamaki tace " Wanne magana ne wannan?" Ta gyara Zama ta kwashe komai ta fada musu, Uncle Babawo yace " That's it! Addua zamuyi nace Miki something smells fishy" Sunata maganan not minding yadda Yaya Shehu yayi shiru deep in thought, se can yace " Inada shawara! Me zai hana ayi Mata aure kunga bashi da wani right over her kenan" Ummiey ta Kai Masa hannu tace " Baka da Kai nawa Afiyya take zakace aure" Mummy ta rike hannun Ummiey yace " A nice idea! Amma waye zai aure ta?" Yaya Shehu ya kaudar da Kai yace " Ni! Ina son ta Zan aureta!!!" Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment 23 Shekaru goma sun wuce a bangaren shi, Yana ganin hakan tamkar satittika goma be Suka wuce. Yakan tuna kamar Wasa yaje yayiwa Fatima asiri Dan ta fita harkar shi ko kuma ya amfani da hakan ya firgita ta saboda Shiga hancin shi da takeyi. Asirin shi ya tonu Malam ya Kama shi dumu dumu da wannan laifin ya Kuma koreshi daga gidan Baki daya. Ya fito daga gidan Babu bacin Rai ko firgici saboda a ganin shi su sukai asara bashi yayi ba, Yana Kuma fatan watarana zasu zo su durkusa har kasa su rokeshi afuwa, su Kuma nemi taimakon shi, Yana tuna fuskar mahaifin shi Malam lokacin da yake fada amsa ya fitar Masa daga gida ya Kuma manta cewar Yana da uba da uwa, wannan abin idan ya tuna Yana Kara saka shi jin kaimin daukar fansa, Yana jin ta kowanne Hali Dole ma se ya dauki fansa, Dole ko sama da kasa zata hadu to tabbas se yayi kudi. Shekarar farko ya dukufa wajen ganin ya tara kudi Dan yayi sustaining living, gang din su Yana nan sede Jarma baban shi ya fahimci halin da ake ciki na korar shi daga makaranta, ranar ya daku a gida ya Kuma saka Yan sanda Suka zo sukai raiding inda suke zaune, huzaifa ya samu ya gudu aka Kama Malam da Junaidu sannan aka bi huzaifa aka Kama shi. Kowa iyayen shi seda suka zo Amma Banda na Junaidu, Baban Jarma na tuhumar su da Bata Musu Dan shi, sun daku akai bailing Malam da huzaifa aka bar Junaidu shi kadai, seda ya kwana biyar sannan huzaifa yazo yayi bailing shi, a ranar sukai gagari min fada a tsakanin su. Tunda sukai bailing shi Bai musu magana ba har sukaje shagon shi, ya Shiga yayi wanka sannan ya fito ya same su duka sunyi daidai, huzaifa ya kunna weed din shi se zukawa yake Yana fesarwa, yayinda Malam ke zaune Yana harhada syrups cikin kwalabe, Jarma wayace hannun shi Yana daddanawa, Bai musu magana ba ya ketare ya saka Kaya sannan ya dawo ya fita Yana jin huzaifa na Masa magana ya Masa banza, Babu jimawa se gashi ya dawo da wuka a hannun shi, gadan gadan ya nufi Jarma da wukar Yana kokarin Burma Masa, cikin hanzari ya Mike tare da cillar da wayar gefe, ya tankwabe hannun Malam syrup din ya malale a kasa, Malam ya dago zaiyi masifa yaga abinda ke hannun Junaidu, ya kwala ihu hakan yasa Jarma ma ya yarda abin da yake hannun shi, Suka fara tsere a Dan karamin shagon, Jarma na fadin " Junaidu me kake Yi hakane, Dan Allah ka aje wukar" Malam ne yayi ta maza ya tsaya Yana fadin " Me mukai maka? Ka yanka ni idan ka Isa Kai Dan iska ne" Wukar hannun shi yasa ya yanke shi damtsen hannunshi, wani ihu ya saki a take jini ya fara zuba, ya dubwsu idanun shi yayi jawur yace " Wannan shi ne magana ta karshe, Rana ta karshe da dayan ki zai Kara zuwa inda nake! Babu ni Babu ku idan ba Haka ba Kuma yadda na yanke shi to kashe mutum zanyi" Jarma ya matso yace " Junaidu me kake fada Wai? Ka fita hankalin ka ne?" Ya Kara matsowa da wukar zai yanke shi yayi baya da sauri, da kyar Jarma ya daure hannun Malam Suka give kowanne mamakin dalilin da yasa Junaidu yin Haka yake, shi Kuma a nashi ganin Babu wani amfani yin kawance dasu. Daga wannan ranar ya koma rayiwar shi daya, baya yiwa kowa magana, ko zaiga dandazon mutane dari to bazai musu sallama ba, massalaci baya zuwa sallar ma bayayi. Ya koma garejin da yake aiki ya cigaba da aiki Yana Tara kudi, sede a wañnan lokacin kudin Babu albarka da kyar yake samu yayi saving na kudin haya, wannan yasa ya fara tunanin zuwa neman saa. Bashi da wani aboki, Bai Kara Neman gida ba, mutanen dake zaune dashi Banda alkabai Babu abinda suke ja Masa da bakunan su, kowa ka tambaya to bazai fada maka abin alkhairi a tattare dashi ba. A hakan shekara ta wuce ya samu da kyar ya biya kudin haya, ya Shiga ta biyu inda ya Kama wata sanaar kuma, wannan hannu bibbiyu da yake se yaga ya fara samun abinda yake nema. A hakan shekaru Suka Kara wucewa, iya aikin makanikanci ya iya wannan dalilin yasa duk yadda ake cewa me gurin ya koreshi saboda munana dabiun shi ya gagara, mutane da yawa idan sun kawo gyaran mota ko abin hawansu zasu ce su Junaidu suke son ya gauara musu Amma ba hakan ke nufi zai musu magana ba ko zai kula su ba. A shekara ta biyar ya hadu da wani Gaye Dan Niger, sunan shi Safiyyu ya hauro daga Niger ya shigo Nigeria, inda ya samu mazauni anan Niger din. Halayen su iri daya ne da Junaidu har gwara Junaidu ma ansan asalin shi Amma shi kuwa kana kallon shi ko a accent dinsa zaka San cewar Dan Niger he's a foreigner. Shagon Dake gefen na Junaidu nan ya kama haya, Babu Wanda kewa wani magana seda akafi wata biyu se yaga kawai Safiyyu ya saya wannan shagunan gaba daya, shi ba aiki ma yakeyi ba hakan ba karamin mamaki da Kuma daga Masa hanakli yayi ba, Amma saboda shi ba ma halin shi bane yiwa mutane magana ba se Bai kula shi ba. Watarana ana zafi Safiyyu ya fito Yana Shan iska shima Junaidu ya fito, suna zaune Babu me magana cikin su, se can Safiyyu yaga Abu ya gilma, ya Mike tsaye ya dubi Junaidu dake faman danne danne a waya yace " Maciji na yawo anan gurin!" Ai tuni ya Mike ya nade sallayya yayi baya Yana kokarin komawa shagon shi Amma ya dakata, jin Safiyyu na fito Babu jimawa Sega macijin a gaban shi, ya tsugguna ya dauka macijin sannan ya murde Masa Kai ya wullar Yana wata irin hatsabibiyar dariya! Junaidu yayi shiru yana jin akwai Wanda ya fishi kenan? Safiyyu ya matso cikin hausar shi ta Yan can yace " Kana bukatar taimako ne?" Junaidu yayi shiru deep in thought with so much hesitation Amma Kuma Yana bukatar yayi kudi ya cika burin shi, " Idan kana bukatar abu, kwankwasa min kawai zakayi!" Ya fada sannan ya wuce ya bar Junaidu tsaye Yana tantanmar abinyi.... AFIYYA is not free, pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment through 09063467258to 0906346725824 Ya Jima a tsaye Yana kokwanton abinda zaiyi, shi duk abin shi yasan maciji is a no place for him, Amma ta Yaya gayen ya dauki wannan macijin ya murde Masa Kai, ya haska fitilar wayar shi yaga tabbas ga ga macijin a yashe a kasa Kai daban Haka gangar jikin daban, ya juya da sauri ya nufi daki ya rufe, yeah shi yasan he's bad idan ana zancen bad guys yasan a kaf kazaure Yana sahun farko to Amma akwai abubuwan da shi yasan bazai iya tunkarar su ba. Hakan yasa ya daina shiga sabgar shi, duk inda yasan zasu hadu ya daina. Kwatsam Yana aiki wani yammaci fada ya hada su shida wani abokin aikin shi, Kuma a gaskiya wancan ne bashi da gaskiya tunda Junaidu idan ka dauke oga zai iya kwana uku ko kanzil Bai cewa wani ba, abinda ya kawo shi kawai yakeyi, kawai Dan ana hirar yanmata da Kuma aure se gayen yace ai wallahi ko kanwar shi zatayi kwantai bazai bawa me Hali irin na Junaidu ba, shi Kuma Junaidu fitowar shi kenan daga kasan wata mota, karaf maganar ta shiga kunnen shi, Yana zuwa kawai Bai ma musu magana ba ya cakumo wuyan rigar shi ya Kai Masa naushi a Baki, Wanda yayi sanadin fashewar bakin jini ya fara zuba. Duka suka taru suna kokarin raba su Wanda da kyar suka samu Suka babanbare rigar Musa daga hannun Junaidu, ya maka Masa harara sannan ya koma ya cigaba da aikin shi, kowa ya Kama abinyi ai Musa se ya fara zage zage Yana fadin ai duk sunsan komai, shi Wanda iyayen shi suka tsine Masa Suka Kore shi, baya sallah baya zuwa massalaci, ta Ina zaiga hasken rayuwa, shida farin ciki se temporary. Maganganu irir iri marasa Dadi hakan ba karamin Bata ran Junaidu yayi ba dukda shi dama kullum zuciyar shi a kusa take, kiris kawai yake jira ya aiwatar da abinda yayi niyyar. Wukar dake gefen wandon shi ya zaro ya nufi Musa Wanda kumfar Baki tasa Bai ma Ankara da abinda ke tunkaro shi ba. Yana zuwa ya samu shafce shi a hannu, ai se jini yace bani guri, Musa ya durkusa tareda rike hannun ya saki kara saboda azabar zafin da ya ratsa kanshi. Ya maida wukar ya cigaba da aikin shi Yana ganin yadda mutane suka taru Amma ko a jikin shi, normally ya kamata ya gudu Amma ko a jikin shi ya cigaba da aikin gaban shi, Wanda suke gurin Suka tafi da Musa asibiti bayan an fadawa cops ai Babu jimawa sukai raiding gurin Basu Sha wahala suka cafke Junaidu se station, wannan Karan shi ne Karo na uku da ya Shiga , Dan hakan ko damuwa baiyi ba Amma yasha azaba a hannun su kamar zasu kashe shi Dan duk sun San shi. A karshe ya kusa sati biyu sannan ana compiling case din zaa kaishi court kawai aka zo da safe aka bude shi ba Wanda ya Masa magana ya fito ya karkade jikin shi, Yana zuwa station ya samu Safiyyu ya hakimce Yana mishi murmushi, " Yallabai ya fito" Ya mike ba tareda yace Musu komai ba ya fita Junaidu ya bi bayan shi shima baice uffan ba, wata mota suka shiga me Asalin kyau, baiyi mamaki ba Dan yasan Babu abinda zai yiwa Safiyyu wahalar mallaka a duniyar nan. Suna zuwa wani gida can gefen inda suke zaune, mamaki sosae Junaidu ya dinga Yi na yadda akai kayan shi ya dawo gidan, Safiyyu ya dube shi yace " Kayi wanka, zaa kawo maka abinci se kazo na fada maka" Har zai fita yaji Junaidu yace " Yanzun nake son jin komai!" Safiyyu ya tsaya yana tattara babbar rigar jikin shi ya daura hannun shi akan sofar kwaya daya Tak dake dakin yace Masa Bayan an Kama shi an tafi dashi, se shugaban su na garage ya Kore shi a aiki, Safiyyu na bacci Yan unguwan thugs suka shigo suka balle shagon Junaidu Suka dinga Masa watsi da kayan shi, Dole tasa Safiyyu ya saya wannan gidan ya dawo da kayan Junaidu zaman. Haka suka fara Zama komai Safiyyu ke providing, shi Kuma Junaidu sede yaci dake duk haukan shi Yana da zuciyar nema yasa ya takura ya samu Safiyyu akan shifa Yana son gaskiya ya samu wani aikin, Yana son Tara kudi, Safiyyu ya nuna Masa hakan ai ba matsala bane zai bashi jari ya fara, Haka ya bashi jari Amma shi Kuma se ya rasa me zaiyi Dan shi sanaar da ya iya kanikanci ce kawai, ganin zai kwari kanshi yasa ya samu Safiyyu yace shi Bai San me zaiyi da wannan kudin ba, yayi dariya yace ya bashi a sati zai dawo Masa da kudin da zai ishe shi bude garage, Junaidu yyai dariya yace ai abune da bazai taba yiwuwa ba, a Haka Suka bar maganar. Kwanaki goma se gashi Safiyyu ya dawo da kudin da Suka says fili, spare parts da sauran kayan gyara, Junaidu ya dinga tambayar shi yadda akai? Sede ya kalleshi proudly yace " Ai na fada maka ka bani lokaci" Junaidu ya kalli Safiyyu yace " Tsoro kake bani" Safiyyu yayi dariya yace " kamar yadda ni kaina tsoro kake bani" Junaidu ya kwashe da adriya wadda ko kadan Bata Masa kyau ba saboda Bai ma Saba Yi ba, mostly murmushi ne shima se ya Dana wani tarkon ko Yana hada mugunta. A hankali ya samu Yara Suka fara aiki a sabon gurin, dukkansu se Suka Saba da yanayin daure fuskar shi, cikin kankanin lokaci gurin yayi fice Junaidu buri ya fara cika, sede hakan Bai Masa ba yafi son yafi Haka, yafi son bawai kazaure kawai ba har jahohin iyaka se sun San da zaman shi da Kuma sanaar da yake, hakan yasa ya samu Safiyyu ya fada mishi Bayan sati Suka dauki hanyar Niger a wani kauye gari karkashin maradi Dan Issa, acan wata irin kebantaccen guri ne Wanda gaba daya Babu kowa it's totally deserted, cikin Sahara nan wata bukka take ita daya, sun Sha tafiya kafin Suka Isa wajen bokan Dan wannan ba malami bane, sun Jima a tare ya bawa Junaidu saa sannan suka sallame shi Suka fito. Bayan nan tabbas yasan yaje gurin malami kafin wani lokaci yayi kudi, yayi fice ko Ina kaje zancen gurin gayranshi ake, a hanakli Safiyyu yayi exposing dinsa to drug selling, ya fara harkar safarar kwayoyi Dan hakan ya Tara arziki na ban mamaki, Babu Wanda ya taba tunanin Yana safarar kwayoyi, bokan su ya tabbatar musu bazaa taba Kama su ba. A shekara ta takwas ya fara neman aure cikin kazauren, daya tashi se ya tafi gidan manya, gidan sarauta sede babanta na fara bincike akan shi ya dakatar dashi, duk yadda yake tunanin zai samu aure a garin Abu ya faskara, da zarar anji labarin shi ne to se a dakatar. Ya girma shekaru sunja, kana kallon shi zakaga a confident man, bazaka taba hango daya daga cikin halayen shi ba Banda girman kai, yadda yake tafiya Yana bada Fadi, zakai tunanin titi ya Masa kadan, Kan shi baya taba sauke shi a kasa sede ya daga sama Yana tafiya. Akwai yarinyar da ya nema Khadija a Roni, magana tayi nisa sosae , watarana yaje zance, gashi da farin jinin Yan Mata sede idan baicw Yana so ba, wasu ma har bin shi suke Haka kallon farko idan mace batai Wasa ba zata iya crushing dinsa ko ma tayi falling Masa gaba daya. Mahaifin ta yazo wuce wa cikin gida ya dawo daga aiki, Junaidu ya Mike kafa Kai kace Dan basarake ne ya hakimce Yana hura hanci, ita Kuma tana zaune gefen shi fuskar ta da dimbin farin ciki tana ta Masa Hira. Baban na zuwa ta mike ta Masa barka da zuwa, yayinda Junaidu ko kallon shi baiyi ba, kafar shi daya Mike yaki tankwashe ta a Haka Baban ya tsallake shi ya wuce, ya Kara fitowa bayan wani lokaci hakance ta kasance. Tana komawa gida yace ai zancen aure ya tashi. AFIYYA One year leap! AFIYYA is not free, pay 300 to 3091721807 First bank of Nigeria Aisha Hassan kwalam, send evidence of payment to 0906346725824 Ya Jima a tsaye Yana kokwanton abinda zaiyi, shi duk abin shi yasan maciji is a no place for him, Amma ta Yaya gayen ya dauki wannan macijin ya murde Masa Kai, ya haska fitilar wayar shi yaga tabbas ga ga macijin a yashe a kasa Kai daban Haka gangar jikin daban, ya juya da sauri ya nufi daki ya rufe, yeah shi yasan he's bad idan ana zancen bad guys yasan a kaf kazaure Yana sahun farko to Amma akwai abubuwan da shi yasan bazai iya tunkarar su ba. Hakan yasa ya daina shiga sabgar shi, duk inda yasan zasu hadu ya daina. Kwatsam Yana aiki wani yammaci fada ya hada su shida wani abokin aikin shi, Kuma a gaskiya wancan ne bashi da gaskiya tunda Junaidu idan ka dauke oga zai iya kwana uku ko kanzil Bai cewa wani ba, abinda ya kawo shi kawai yakeyi, kawai Dan ana hirar yanmata da Kuma aure se gayen yace ai wallahi ko kanwar shi zatayi kwantai bazai bawa me Hali irin na Junaidu ba, shi Kuma Junaidu fitowar shi kenan daga kasan wata mota, karaf maganar ta shiga kunnen shi, Yana zuwa kawai Bai ma musu magana ba ya cakumo wuyan rigar shi ya Kai Masa naushi a Baki, Wanda yayi sanadin fashewar bakin jini ya fara zuba. Duka suka taru suna kokarin raba su Wanda da kyar suka samu Suka babanbare rigar Musa daga hannun Junaidu, ya maka Masa harara sannan ya koma ya cigaba da aikin shi, kowa ya Kama abinyi ai Musa se ya fara zage zage Yana fadin ai duk sunsan komai, shi Wanda iyayen shi suka tsine Masa Suka Kore shi, baya sallah baya zuwa massalaci, ta Ina zaiga hasken rayuwa, shida farin ciki se temporary. Maganganu irir iri marasa Dadi hakan ba karamin Bata ran Junaidu yayi ba dukda shi dama kullum zuciyar shi a kusa take, kiris kawai yake jira ya aiwatar da abinda yayi niyyar. Wukar dake gefen wandon shi ya zaro ya nufi Musa Wanda kumfar Baki tasa Bai ma Ankara da abinda ke tunkaro shi ba. Yana zuwa ya samu shafce shi a hannu, ai se jini yace bani guri, Musa ya durkusa tareda rike hannun ya saki kara saboda azabar zafin da ya ratsa kanshi. Ya maida wukar ya cigaba da aikin shi Yana ganin yadda mutane suka taru Amma ko a jikin shi, normally ya kamata ya gudu Amma ko a jikin shi ya cigaba da aikin gaban shi, Wanda suke gurin Suka tafi da Musa asibiti bayan an fadawa cops ai Babu jimawa sukai raiding gurin Basu Sha wahala suka cafke Junaidu se station, wannan Karan shi ne Karo na uku da ya Shiga , Dan hakan ko damuwa baiyi ba Amma yasha azaba a hannun su kamar zasu kashe shi Dan duk sun San shi. A karshe ya kusa sati biyu sannan ana compiling case din zaa kaishi court kawai aka zo da safe aka bude shi ba Wanda ya Masa magana ya fito ya karkade jikin shi, Yana zuwa station ya samu Safiyyu ya hakimce Yana mishi murmushi, " Yallabai ya fito" Ya mike ba tareda yace Musu komai ba ya fita Junaidu ya bi bayan shi shima baice uffan ba, wata mota suka shiga me Asalin kyau, baiyi mamaki ba Dan yasan Babu abinda zai yiwa Safiyyu wahalar mallaka a duniyar nan. Suna zuwa wani gida can gefen inda suke zaune, mamaki sosae Junaidu ya dinga Yi na yadda akai kayan shi ya dawo gidan, Safiyyu ya dube shi yace " Kayi wanka, zaa kawo maka abinci se kazo na fada maka" Har zai fita yaji Junaidu yace " Yanzun nake son jin komai!" Safiyyu ya tsaya yana tattara babbar rigar jikin shi ya daura hannun shi akan sofar kwaya daya Tak dake dakin yace Masa Bayan an Kama shi an tafi dashi, se shugaban su na garage ya Kore shi a aiki, Safiyyu na bacci Yan unguwan thugs suka shigo suka balle shagon Junaidu Suka dinga Masa watsi da kayan shi, Dole tasa Safiyyu ya saya wannan gidan ya dawo da kayan Junaidu zaman. Haka suka fara Zama komai Safiyyu ke providing, shi Kuma Junaidu sede yaci dake duk haukan shi Yana da zuciyar nema yasa ya takura ya samu Safiyyu akan shifa Yana son gaskiya ya samu wani aikin, Yana son Tara kudi, Safiyyu ya nuna Masa hakan ai ba matsala bane zai bashi jari ya fara, Haka ya bashi jari Amma shi Kuma se ya rasa me zaiyi Dan shi sanaar da ya iya kanikanci ce kawai, ganin zai kwari kanshi yasa ya samu Safiyyu yace shi Bai San me zaiyi da wannan kudin ba, yayi dariya yace ya bashi a sati zai dawo Masa da kudin da zai ishe shi bude garage, Junaidu yyai dariya yace ai abune da bazai taba yiwuwa ba, a Haka Suka bar maganar. Kwanaki goma se gashi Safiyyu ya dawo da kudin da Suka says fili, spare parts da sauran kayan gyara, Junaidu ya dinga tambayar shi yadda akai? Sede ya kalleshi proudly yace " Ai na fada maka ka bani lokaci" Junaidu ya kalli Safiyyu yace " Tsoro kake bani" Safiyyu yayi dariya yace " kamar yadda ni kaina tsoro kake bani" Junaidu ya kwashe da adriya wadda ko kadan Bata Masa kyau ba saboda Bai ma Saba Yi ba, mostly murmushi ne shima se ya Dana wani tarkon ko Yana hada mugunta. A hankali ya samu Yara Suka fara aiki a sabon gurin, dukkansu se Suka Saba da yanayin daure fuskar shi, cikin kankanin lokaci gurin yayi fice Junaidu buri ya fara cika, sede hakan Bai Masa ba yafi son yafi Haka, yafi son bawai kazaure kawai ba har jahohin iyaka se sun San da zaman shi da Kuma sanaar da yake, hakan yasa ya samu Safiyyu ya fada mishi Bayan sati Suka dauki hanyar Niger a wani kauye gari karkashin maradi Dan Issa, acan wata irin kebantaccen guri ne Wanda gaba daya Babu kowa it's totally deserted, cikin Sahara nan wata bukka take ita daya, sun Sha tafiya kafin Suka Isa wajen bokan Dan wannan ba malami bane, sun Jima a tare ya bawa Junaidu saa sannan suka sallame shi Suka fito. Bayan nan tabbas yasan yaje gurin malami kafin wani lokaci yayi kudi, yayi fice ko Ina kaje zancen gurin gayranshi ake, a hanakli Safiyyu yayi exposing dinsa to drug selling, ya fara harkar safarar kwayoyi Dan hakan ya Tara arziki na ban mamaki, Babu Wanda ya taba tunanin Yana safarar kwayoyi, bokan su ya tabbatar musu bazaa taba Kama su ba. A shekara ta takwas ya fara neman aure cikin kazauren, daya tashi se ya tafi gidan manya, gidan sarauta sede babanta na fara bincike akan shi ya dakatar dashi, duk yadda yake tunanin zai samu aure a garin Abu ya faskara, da zarar anji labarin shi ne to se a dakatar. Ya girma shekaru sunja, kana kallon shi zakaga a confident man, bazaka taba hango daya daga cikin halayen shi ba Banda girman kai, yadda yake tafiya Yana bada Fadi, zakai tunanin titi ya Masa kadan, Kan shi baya taba sauke shi a kasa sede ya daga sama Yana tafiya. Akwai yarinyar da ya nema Khadija a Roni, magana tayi nisa sosae , watarana yaje zance, gashi da farin jinin Yan Mata sede idan baicw Yana so ba, wasu ma har bin shi suke Haka kallon farko idan mace batai Wasa ba zata iya crushing dinsa ko ma tayi falling Masa gaba daya. Mahaifin ta yazo wuce wa cikin gida ya dawo daga aiki, Junaidu ya Mike kafa Kai kace Dan basarake ne ya hakimce Yana hura hanci, ita Kuma tana zaune gefen shi fuskar ta da dimbin farin ciki tana ta Masa Hira. Baban na zuwa ta mike ta Masa barka da zuwa, yayinda Junaidu ko kallon shi baiyi ba, kafar shi daya Mike yaki tankwashe ta a Haka Baban ya tsallake shi ya wuce, ya Kara fitowa bayan wani lokaci hakance ta kasance. Tana komawa gida yace ai zancen aure ya tashi. AFIYYA One year leap! AFIYYA is not free, pay 300 to 3091721807 First bank of Nigeria Aisha Hassan kwalam, send evidence of payment to 0906346725823 Shekaru goma sun wuce a bangaren shi, Yana ganin hakan tamkar satittika goma be Suka wuce. Yakan tuna kamar Wasa yaje yayiwa Fatima asiri Dan ta fita harkar shi ko kuma ya amfani da hakan ya firgita ta saboda Shiga hancin shi da takeyi. Asirin shi ya tonu Malam ya Kama shi dumu dumu da wannan laifin ya Kuma koreshi daga gidan Baki daya. Ya fito daga gidan Babu bacin Rai ko firgici saboda a ganin shi su sukai asara bashi yayi ba, Yana Kuma fatan watarana zasu zo su durkusa har kasa su rokeshi afuwa, su Kuma nemi taimakon shi, Yana tuna fuskar mahaifin shi Malam lokacin da yake fada amsa ya fitar Masa daga gida ya Kuma manta cewar Yana da uba da uwa, wannan abin idan ya tuna Yana Kara saka shi jin kaimin daukar fansa, Yana jin ta kowanne Hali Dole ma se ya dauki fansa, Dole ko sama da kasa zata hadu to tabbas se yayi kudi. Shekarar farko ya dukufa wajen ganin ya tara kudi Dan yayi sustaining living, gang din su Yana nan sede Jarma baban shi ya fahimci halin da ake ciki na korar shi daga makaranta, ranar ya daku a gida ya Kuma saka Yan sanda Suka zo sukai raiding inda suke zaune, huzaifa ya samu ya gudu aka Kama Malam da Junaidu sannan aka bi huzaifa aka Kama shi. Kowa iyayen shi seda suka zo Amma Banda na Junaidu, Baban Jarma na tuhumar su da Bata Musu Dan shi, sun daku akai bailing Malam da huzaifa aka bar Junaidu shi kadai, seda ya kwana biyar sannan huzaifa yazo yayi bailing shi, a ranar sukai gagari min fada a tsakanin su. Tunda sukai bailing shi Bai musu magana ba har sukaje shagon shi, ya Shiga yayi wanka sannan ya fito ya same su duka sunyi daidai, huzaifa ya kunna weed din shi se zukawa yake Yana fesarwa, yayinda Malam ke zaune Yana harhada syrups cikin kwalabe, Jarma wayace hannun shi Yana daddanawa, Bai musu magana ba ya ketare ya saka Kaya sannan ya dawo ya fita Yana jin huzaifa na Masa magana ya Masa banza, Babu jimawa se gashi ya dawo da wuka a hannun shi, gadan gadan ya nufi Jarma da wukar Yana kokarin Burma Masa, cikin hanzari ya Mike tare da cillar da wayar gefe, ya tankwabe hannun Malam syrup din ya malale a kasa, Malam ya dago zaiyi masifa yaga abinda ke hannun Junaidu, ya kwala ihu hakan yasa Jarma ma ya yarda abin da yake hannun shi, Suka fara tsere a Dan karamin shagon, Jarma na fadin " Junaidu me kake Yi hakane, Dan Allah ka aje wukar" Malam ne yayi ta maza ya tsaya Yana fadin " Me mukai maka? Ka yanka ni idan ka Isa Kai Dan iska ne" Wukar hannun shi yasa ya yanke shi damtsen hannunshi, wani ihu ya saki a take jini ya fara zuba, ya dubwsu idanun shi yayi jawur yace " Wannan shi ne magana ta karshe, Rana ta karshe da dayan ki zai Kara zuwa inda nake! Babu ni Babu ku idan ba Haka ba Kuma yadda na yanke shi to kashe mutum zanyi" Jarma ya matso yace " Junaidu me kake fada Wai? Ka fita hankalin ka ne?" Ya Kara matsowa da wukar zai yanke shi yayi baya da sauri, da kyar Jarma ya daure hannun Malam Suka give kowanne mamakin dalilin da yasa Junaidu yin Haka yake, shi Kuma a nashi ganin Babu wani amfani yin kawance dasu. Daga wannan ranar ya koma rayiwar shi daya, baya yiwa kowa magana, ko zaiga dandazon mutane dari to bazai musu sallama ba, massalaci baya zuwa sallar ma bayayi. Ya koma garejin da yake aiki ya cigaba da aiki Yana Tara kudi, sede a wañnan lokacin kudin Babu albarka da kyar yake samu yayi saving na kudin haya, wannan yasa ya fara tunanin zuwa neman saa. Bashi da wani aboki, Bai Kara Neman gida ba, mutanen dake zaune dashi Banda alkabai Babu abinda suke ja Masa da bakunan su, kowa ka tambaya to bazai fada maka abin alkhairi a tattare dashi ba. A hakan shekara ta wuce ya samu da kyar ya biya kudin haya, ya Shiga ta biyu inda ya Kama wata sanaar kuma, wannan hannu bibbiyu da yake se yaga ya fara samun abinda yake nema. A hakan shekaru Suka Kara wucewa, iya aikin makanikanci ya iya wannan dalilin yasa duk yadda ake cewa me gurin ya koreshi saboda munana dabiun shi ya gagara, mutane da yawa idan sun kawo gyaran mota ko abin hawansu zasu ce su Junaidu suke son ya gauara musu Amma ba hakan ke nufi zai musu magana ba ko zai kula su ba. A shekara ta biyar ya hadu da wani Gaye Dan Niger, sunan shi Safiyyu ya hauro daga Niger ya shigo Nigeria, inda ya samu mazauni anan Niger din. Halayen su iri daya ne da Junaidu har gwara Junaidu ma ansan asalin shi Amma shi kuwa kana kallon shi ko a accent dinsa zaka San cewar Dan Niger he's a foreigner. Shagon Dake gefen na Junaidu nan ya kama haya, Babu Wanda kewa wani magana seda akafi wata biyu se yaga kawai Safiyyu ya saya wannan shagunan gaba daya, shi ba aiki ma yakeyi ba hakan ba karamin mamaki da Kuma daga Masa hanakli yayi ba, Amma saboda shi ba ma halin shi bane yiwa mutane magana ba se Bai kula shi ba. Watarana ana zafi Safiyyu ya fito Yana Shan iska shima Junaidu ya fito, suna zaune Babu me magana cikin su, se can Safiyyu yaga Abu ya gilma, ya Mike tsaye ya dubi Junaidu dake faman danne danne a waya yace " Maciji na yawo anan gurin!" Ai tuni ya Mike ya nade sallayya yayi baya Yana kokarin komawa shagon shi Amma ya dakata, jin Safiyyu na fito Babu jimawa Sega macijin a gaban shi, ya tsugguna ya dauka macijin sannan ya murde Masa Kai ya wullar Yana wata irin hatsabibiyar dariya! Junaidu yayi shiru yana jin akwai Wanda ya fishi kenan? Safiyyu ya matso cikin hausar shi ta Yan can yace " Kana bukatar taimako ne?" Junaidu yayi shiru deep in thought with so much hesitation Amma Kuma Yana bukatar yayi kudi ya cika burin shi, " Idan kana bukatar abu, kwankwasa min kawai zakayi!" Ya fada sannan ya wuce ya bar Junaidu tsaye Yana tantanmar abinyi.... AFIYYA is not free, pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment through 0906346725825 Kamar Wasa Sega shekara daya tazo ta wuce, se gashi har nazo Wai na gama secondary school, abin har mamamki yake bani, ranar da na fito daga food and nuts wadda ita ce last paper, nayi submitting sannan na fito na tsaya a gaban varender class dinmu Ina kallon admin block kamar ranar aka kawo ni Amma gashi har shekaru uku sun wuce, duniya zancen banza na ayyana a raina, Abbu ya fado min I remembered ranar Dana Gama primary school dina, na dawo na samu baya gida nayi ta kuka saboda nasan ya kamata ace Yana gida Yana Jirana, koma shi ne yaje ya dakko ni daga school. Nanny dake zaune a parlor se kallona kawai take Amma Bata ma bani hakuri ba, hakan ya Kara tunzura ni na tafi daki Amma Ina zuwa se Naga traveling bag dita a aje, na Isa gurin Amma kafin na bude na hango wrapped box da ribbon a sama, nayi sauri na karasa na yage, na kankame visa din zuwa Berlin Germany, se ticket dina Wanda take reading time of flight baifi awa daya da rabi ya rage ba. Na sauri na cire kayan jikina nayi wanka, Ina fitowa na samu Nanny ta fito da kayan da Zan saka , na saka na janyo kayan na fito na samu Abbu a tsaye Yana tamin murmushi....Kaina na juyar gefe Ina goge hawayen da ya gangaro min, ana mantawa da abubuwa da dama Amma bazan taba mantawa da Abbu ba, memories din shi will forever be fresh cikin zuciyata. Na sauka Ina tafiya a hankali Dan fita daga makarantar ba tareda na jira ko daya daga cikin Yan ajin mu sun fito munyi sallama ba. Tunda dukkan su within Ringim vicinity suke to watarana zamu hadu. Na cigaba da tafiya a hankali har na karasa gida, zuciyata tayimin nauyi sosae, Ina karasawa kofar gida na samu Babu kowa a kofar gidan, na saka kaina na Shiga na samu Ummaan su a zaune tana waya, hannun ta tasa ta tsayar Dani na tsaya na jira har ta gama wayar tace min, me ya dawo dake? Na kalleta da alamar rashin fahimta nace " Na Gama exams din ai" Ta tabe baki tace " Se kizo ki daura abinci, kinsan Allah akan Ina Miki magana kina zare min idanu zanci ubanki, ni Saar kice Zan na Miki magana kina amsa ni yadda kike so, Dan Kinga kin girma ko?" Bance Mata komai ba na juya na shiga daki, na cire uniform dina na saka wata bakar soft morning gown da ta kode saboda kullum ita nake sakawa idan zanyi aiki, Zan fito Naga wani karamin wrapped parcel a gefen kayana, na karasa na yage parcel din se ya greeting card ya bayyana da kwalin turare, na aje jin Kirana da Ummaan su keyi, na wuce Bayan na zura kayan cikin na fito na nufi mangal da aka samu Yaya ya siyo min danyi moving to gawayi min bar itace. Na hada na hura hayakin ya dake ni, nayi saurin mikewa na dakko tukunya na daura sannan na koma na Kama jajjage, Ina nan Ina aikin se naji sallamar Hafsa ta shigo, a gabana ta tsaya tare da rungume ni tace " Congratulations Afiyya, Allah ya sanya alkhairi!" Se naji dadi cikin Raina tunda na dawo ba Wanda yamin makamancin abinda ta yimin, nayi murmushi nace " Nagode Hafsisi. Kije ki cire uniform din " Ta amsa ni sannan ta shige ciki, Babu jimawa na kammalla abinci na koma daki lokacin Hafsa ta koma dakin Babar su, na ciro kayan na bude greeting card din, idanuna Suka sauka akan short note da aka rubuta jikin card din da bakin pen, Babu tantama Yaya ne dan shi ne me using black pen. Ma saki sirirn murmushi na fara karantawa, idanuna Suka Kara haske saboda yadda zuciyata ke wani tsallen murna, he confessed Yana Sona, na kankame card din a kirjina Ina jin wani sanyin Dadi Yana bin dukkan gabban jikina, hawaye ya sakko min daga idanuna, tabbas soyayyar shi itace abar da ta dinga bani karfin gwiwa cigaba da Zama dasu, na sani zuciyata shi take so sede takan tuna min lokaci zuwa lokaci akan nayi a hankali kada se na zarma yazo bama Sona yake ba ko Kuma iyayen shi Suki amincewa . Amma duk da Haka kullum Rana Kara son shi nake har wancan watan Nanny da tazo seda ta fahimci hakan, muna Hira da yamma Ina taje kaina tace " Soyayya kuke keda Yaya ne?" Na Dan kalleta da sauri se Kuma na rasa abinda zance Mata tunda ni ban iya karya ba, ko nayi karya ma se an gane karya nake, tace " Hakane kenan ko?" Na gyada Mata kaina, tayi shiru Wanda yasa gaba daya naji na takura, se nayi saurin daure kaina na fita tsakar gida Dan awkwardness din baya min dadi, se dare min kwanta tace min " Yaya mutumin arziki ne, yaro ne na gari Dan albarka, shi mutum ne da nake da tabbacin ba zai cuceki ba, Kuma da auren ku zai kasance da zanfi kowa murna Kuma hankalina zai kwanta nasan kina hannu nagari, sede Afiyya Ina tsoron abinda zaije ya dawo, Ina tsoron idan iyayen shi zasu amince ko Kuma kawunnan ki zasu amince dashi" Na Dan gyara kwanciyata Ina jin words dinta suna sinking cikin kaina nace " To kiyi min addua Amma ni Ina son shi gaskiya" Se batace min komai ba a Haka mukai shiru bacci ya daukeni daga nan. Jin motsi yasa na rufe card din na aje na samu turaren na fesa kamshin so sweet, nayi murmushi Ina jin duk wata kewa da nake ta ragu. Da yamma Ina zaune gaban Miya da maburgi a hannuna naji sallama, Ummaan su ta dubi Hafsa dake gefen ta tace ta duba waye, kafin ma ta Kai ga fita, Sega masu sallamar sun shigo, Yan Mata ne guda biyu sun Sha kyau abinsu, Ummaan ta fara musu barka da zuwa, su Kuma se kalle kalle suke suna yatsina fuska kamar sunga kashi, but ba se an fada maka ba kana kallon su kaga yayan masu kudi, ta kalleni tace " Se nace a kawo tabarma?" Na aje maburgin hannuna na nufi daki Dan dakkowa naji daya daga ciki tana fadin " No need kawai! Sako aka Aiko Wai a bawa Afiyya!" Na juyo na kallesu da kyau lokacin na fahimci ai nasan daya daga ciki, she's called Shahida na Dan taba ganin ta gidan su Rooks sau daya. Umman su najin Haka ta Bata fuska tace " Se ku Bata ai gata nan!" Na dube su nace " Sako from where?" Dayar da ba Shahida din ba tace " Istanbul" Suka Mika min katuwar Leda, na karba na musu godiya suka juya Suka tafi, Nima na nufi daki Dan ajewa tace min na dawo na kawo ledar, ko musawa banyi ba na aje Mata ledar na juya na koma aikin burge miyar, ko Kara kallon gurin banyi ba, idan da sabo ai na Saba, shekara uku da wani abun ba kwanaki uku bace ba. Ina jin yadda Hafsa ke exclamation na kyan only God knows what! Na sauke miyar na juye gawayin a gaban rijiya na kashe sannan na tattara na aje inda nake adanawa, na dawo Zan wuce naji sallamar Yaya,cikin sauri na juya fuskata dauke da murmushi nace " Yaya!" Ya kalleni Yana min wink tareda sakar min tattausan murmushi Amma Bai amsa ni ba, se ya nufi wajen Babar shi, ta riga ta hade kayan kafin ya karaso ta kalleni tace " Zo ki dauke tsiyar ki!" Na karasa na dauki ledar na nufi daki Ina jin kaifin idanun Yaya da ya bini dasu, na zauna na fara Ciro kayan dake ciki, waya ce me kyau kirar infinix sabuwa dal cikin kwalin ta, se turarrruka masu kyau Wanda kwalin kawai abin kallo ne. Se abaya da takalmi a ciki. A kasan kayan Naga small paper It's your graduation today, you know that u always in my thoughts for a second I never forget you. I hope you will like the gift. Please give me a call after! Shehu Matawalle! Nayi murmushi Ina Kara kallon kayan, shi Bai manta Dani ba na ayyana cikin raina, gashi ni tsakani da Allah na manta dashi gaba daya. Ture kayan nayi daga gabana na aje paper, Hafsa ta shigo ta zauna gefena tace " Saurayin ki ne ya Aiko Miki?" Nayi dariya nace " Wai ke ba gidan Siyama naji ance zakije ba" Ta mike tana zumbura Baki tace " Na tafi!" Na Bata sakon ta gaida Siyama wadda daga baya tayi aure tana zaune acan sabon gari. Bayan sallar maghrib na samu na sulale na fita kamar yadda nakeyi, daga can gefe Yana tsaye Yana kallon kofar gida na Isa inda yake tsaye nace " Yayana!" Ya juyo Yana kallona fuskar shi dauke da murmushi me kwantar min da hankali yace "Afeey ta! Congratulations know that wannan shi ne starting point, Inshaaa Allah Zan tsaya Miki Naga kinyi karatu" Nayi murmushi nace " Zanyi farin ciki kuwa, saboda Ina son cika burin Abbuna, I've received your gift I'm grateful" Yayi min murmushi yace " Inshallah! Kayan meye Ummaan mu ta baki dazun Dana shigo?" Na gyara tsayuwa ta na fada Masa daga gurin Yaya Shehu ne, ya Bata fuska yace " Ai nace Zan siya Miki waya ko ba Haka ba?" Na Dan rausayar da kaina nace " To ai bani nace ya kawo min ba, he felt like ya aiko se kayi godiya Mana" Ya Kara tamke fuska yce " Kinsan I don't like you with that guy ko?..." Nayi saurin katse shi nace " Because?" " Saboda yadda yake kallon ki Yana nuna sonki yake, Kuma I'm sure kin fahimci hakan kawai pretense ne." Yanayina ya Dan canja nace " To ai shikenan!" " And what's that? Kenan kinsan Yana son naki ko?" Na hade hannayena alamar gajiya da maganar nace " Please Yaya! Kai kasan Kai nake so, Kai kadai nake kulawa, so kana ganin zaka hana wani yace Yana Sona ne? It will not be, Abu me muhimmancin shi ne Kai nake so ba wani ba!" Ina Gama fadar hakan na juya na wuce gida, Ina jin shi Yana Kirana na Masa banza, matsalata dashi kenan Babu dama wani yayi min magana ranar Haka zai wuni Yana fushi, yayi ta mita kenan. Ina zuwa tsakiyar gidan aka kawo wuta, gaba daya tsakar gidan ya dauki haske gani Kuma a tsakiyar gida sanye da hijabi, Ummaan su na zaune kofar dakin ta, ta zuba min idanu tana kallona!!! Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 First bank of Nigeria A'isha Hassan kwalam, send evidence of payment to 09063467258.26 Ban taba jin tsoro ba kamar yadda naji a wannan lokacin ba, idanuna a warwaje na zuba Mata idanu Ina jiran abinda zata ce, nasan na kade Tau har ganyena. Ta mike tana kallona har ta karaso inda na tsaya na kasa motsawa, kafin na ankare ta dauke ni da Mari Wanda saukar shi seda tasa na matsa daga gurin saboda it landed unexpected " Dama so nake na Kama ki da kaina, ai nasan kina fita. Gidan uban wa kike zuwa?" Nayi shiru Ina rike da kuncina, Ina zance Mata naje? Ko Ina Wasa da wuta bazan ce gurin Yaya nake zuwa ba, balle ko na fada ma nasan bazata yadda ba. Jin nayi shiru ta Kai min wani dukan, na tsugunna a gurin na saki kuka, tasa kafarta ta hanbare ni " Shiru shiru dake kamar ba Zaki aikata ba, dama nasan wannan nunkunfurcin da kike bana Allah bane, Zakici ubanki a cikin gidannan!" Jan takalmin da naji yasa na Kara sakin kuka Dan nasan na Gama yawo Kawu Sa'idu ne, ba zai taba daga kafa yayi tafiya yadda ake Yi ba, sede ya dinga Jan takalmin sharaf sharaf, nayi saurin mikewa tasa kafarta ta maida ni , saboda yadda ta taka kafar tawa yasa naji zafi ya ratsa jikina har na saki karamar Kara. " Gata nan! Dama na fada maka fita take Yi kaki yarda, gata yanzun dai ka ganta da hijabi, to shigowar ta kenan daga yawon ta zubar!" Banma San meye yawon ta zubar din ba Amma nasan tabbas ba Abu ne decent ba, tsugunnawa yayi Yana fuskanta ta yace " Ina Kika je?" Na girgiza kaina sede bazan iya cewa komai ba, yasa hannun shi ya kwada min Mari Wanda da farko nayi tunanin fuskata ta fashe, na saki Kara Ina jin wani dum! A kunnena, ya Kara matsowa ni Kuma nayi saurin Jan jikina bayana yace " Ina Kika je? Iskanci Kika fara? To baa gidana ba muna tausayin maraicin ki Ashe ke Baki tausayin kanki, to aure zanyi Miki tun kafin ki dakko min abun kunya" Yadda kalmar aure zai min ta dake ni na Kuma ji zafin saukar ta bana tunanin naji zafin Marin da Suka min, na fara kuka sosae Ina fadin " Wallahi Kawu ba abinda kuke tunani bane! Allah kofar gida kawai naje. Allah Kawu ka yarda Dani" Ni kaina kukan da nake was breaking me, zuciyata ji nake kamar an watsa min ruwan zafi, tun farkon da nake sneaking nake fita to meet Yaya nasan I was making a lot big mistake Amma saboda yadda nake son shi ban mayi kokarin danne zuciyata ba, shi yace min Yana son abun ya Zama a little secret between us saboda yasan iyayen shi zaiyi wuya su amince da maganar auren mu, plus yana ganin idan maganar ta fito zasu ga ai har na Kai shekarun da zanyi soyayya, kenan na Isa aure! Duk tambaya daya se ya mareni, saboda mugunta se ta rike min hannayena ta baya yadda bazan iya karewa ba, tun Ina kokarin kwatar kaina har na daina se hawaye da ya dinga bin kuncina, naji fuskata ko Ina radadi kawai yakeyi kamar an zuba min borkono. Se daya ji marin ya ishe shi sannan yace ta sakeni, ta sakeni na kallesu tsabar su ta Kara nunkuwa cikin zuciyata, yanayin fuskar Ummaan su kawai na kalla nasan farin ciki take. " Ba Zaki tashi ki bace min anan ba?" Nayi saurin mikewa Zan nufi daki naji Ummaan tace " taje Ina Kuma? Ai asibiti zaa kaita amata gwajin ciki, ta Yaya na fada maka wannan ba shi ne Karo na farko da take fita ba, na kyalleta ne Naga gudun ruwanta!" Se Naga Kawu ya kalleni fuskar shi da wasi wasi Amma Dan ya faranta ran matar shi Haka ya Jani ya tasa keyata muka tafi wani Rahma clinic dake nan kusa damu, Banda kukan fili Dana zuci Babu abinda nakeyi, Muna zuwa Babu mutane Dan haka na shiga dakin scan din, likitan na zaune da wayar shi a hannu alamu sun nuna ya Jima Babu patient. Kawu ya samu guri ya zauna tareda fadin " Likita zargi muke tana da ciki saboda yawon banza da take..." Babu shiri doctor ya dubeni sannan ya dubi kawu da yayi dare dare a kujera, hawaye Suka Kara gudu akan fuskata, baa taba cimin mutunci irin wannan ba. Doctor y dubi Kawu Sa'idu yace ya bamu guri, bayan ya fita yace na hau gadon Babu musu na hau ya zuba min gel cikin bare cikina Wanda seda taikar jikina ta tashi saboda sanyin shi, ya dauki pointer ya dinga gogagwa akan gel din da ya bawa light rays din damar penetrating cikin cikina, seda ya Gama ya Mika min tissue na goge cikina naja rigata sannan yace " Amina! Waye wancan mutumin? Me ye hadin ki dashi" Nayi mishi shiru se kawia kallon shi da nake a raina Ina saka meye amfanin fada Masa? Maganin me zai min? Yayi yayi nayi magana naki, se kuka da nakeyi Wanda Ina jin azabar ciwo da kaina keyi, zugin da fuskata takeyi da Kuma dum da kunne na yayi, har na mutu bazan manta da wannan ranar ba. Ganin ba zanyi magana ba ya fita ya bawa Kawu Sa'idu sakamakon sannan yace Masa ai alada ma nakeyi, ya Kuma San Babu yadda zaayi me ciki tayi period. Daga Haka muka juya zuwa gida, a hanya yace min " Ba dai abin kunya Zaki jawo min ba, to aure zanyi Miki! Aure Zan Miki se kije ki dandana abinda kowa yakeji" Bance Masa komai ba Dan banida bakin maganar, plus ban masan me zance Masa ba, roko na riga na roke shi na Kuma fada musu iyakar gaskiya ta, kuskure nasan nayi Amma I don't deserve abinda akai min. Muna zuwa gida na tarar da Yaya, Baba da Hafsa da umman su sunyi cirko cirko kamar zakaru. Muna hada idanu dashi na Kara sakin kuka, Kawu yayi tsaki ya fada Mata sakamakon scan din da nayi, ta tabe baki tace " Ni fa bazan taba yarda fitar da yarinyar nan take ba shagon wani namijin take zuwa ba! Yadda kace kawai kayi Mata aure shi ne maslaha!" Na dubi Yaya da gaba daya fuskar shi tayi turning pale saboda tsabar tashin hankali, idanuna na saka cikin nashi Ina rokon shi ya fada musu gurin shi nake zuwa, amma se ya kaudar da kanshi gefe, karshe ma daki ya tafi abin shi ya barni nan tsaye. Na bi Bayan shi da kallo cikeda madaukakin mamaki, how do you want me to believe cewar Yaya ya juya bayan shi a kaina, ya kasa fitowa yace dashi muke haduwa , in fact shi ya kawo shawarar Ina fita Dan mu hadu. Zuciyata naji tana bugawa da karfin gaske tamkar zata balla kirjina ta fito, hawayen dake ta suntiri a fuskata na neme su na rasa, what's the worst feeling better than been betrayed? Ina ganin shi ne worst feeling Dana taba ji a rayuwata. A wannan Daren nayi kuka kamar Zan cire idanuna, at some point na tuhumi rayuwa da yin walagigi da ni, nayi kuka na rashin madafa, na rashin gata, na rashin abinyi! Afiyya is not free pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment through 0906346725827 Bana tunanin na taba ganin dare me tsawon wannan Daren, har so nake gari ya waye tunda nasan bazan iya bacci ba. Kukan ma ya daina zuwa, there are times a cikin rayuwar ka da kake jin komai baya tafiya daidai Kuma baka saka ran wani relief zai taba zuwa, to Haka naji, naji zuciyata ta bushe, naji I was equal and ready to whatsoever comes up, menene a rayuwa? Kin Dadi to ni nasan na Gama jin Dadi. Na mike na duba tab dita da na dakko nake amfani da ita a boye Naga biyu da rabi na dare se kawai na fita tsakar gida nayi alwala, na Jima a tsaye Ina jin iska me dadi tana kadawa, a raina nayi wishing, Ina ma dai ace matsalolina zasu bi iskar nan su tafi? Na dubi sama yadda tayi blue me kyau, ga taurari da Suka cika ta Suka kawata saman. A lokaci daya na furta subhannallah! Se naji karfin gwiwar yin addua ya kamani, na koma daki na tada sallah amma Dana idar zanyi addua se na gagara yi, na fara kuka cikin zuciyata abubuwa tari ne barkatai a ciki, da tarin bukatu a ciki, Amma bakina se yayi nauyin furta Haka, Abu daya ya kwantar min da hanakli nasan Allah yafi kowa sanin bukata ta. Kada na cika ku da wannan maganar,asuba nayi a kunnena na fito nayi sallah sannan na gyara dakin, I wanted something to distract my mind away. Nayi shara nayi wanke wanke sannan na kunna murhi nayi dumamen tuwo na dama koko. Ta lungun dakin ta anan gawayi yake se na tafi dakkowa Dan na Kara na daura musu ruwan wanka, tun a kofar dakinta nasan Kawu Sa'idu Bai fita ba saboda takalman sa na gurin. Na Gama dibar gawayin naji tana fadin " To ya zaka cewa Yan uwanka, kasan Dole zasu ki maganar auren" Ya saki dariyar da naji tamkar ruwan zafi take cikin zuciyata yace " Zance musu maza take bi, shiyasa" " Ba zasu yarda ba, kaima ka sani! Shi mutmunin da kake fada zaka aura Mata yaushe zai zo?" " Tunda yau Zaki fita na fada Masa ya zo gobe" Jikina ya fara rawa nayi saurin barin gurin, da gaske ban kawo zai iya yimin aure ba, ban taba kawowa cewar Bayan wannan mummunar rayuwar da nayi ba Ashe akwai wata dake jirana ba. Na karasa komai nayi wanka na koma daki abincin ma ban ci ba Dan I'm not in the mood, bana ma jin yunwar. Ina zaune ta kwala min Kira tace min na daura abincin Rana saura Kuma idan na ga dama na Kara fita, abin da aikai min jiya ba komai ba me, sannan idan naga dama in Zama cikin shiri sati daya kawai ya rage a daura min aure. Wannan maganar ta girgiza rayuwa ta, a hankali na koma daki na zauna tareda runtse idanuna Ina tunanin aure zaayi min da gaske, nidai bana son auren tabbas, fada ma Bata Baki ne Amma Kuma ya zanyi. Motsi naji a kofar dakin Wanda yasa na juyo da sauri Amma ganin Yaya ne yasa na maida kaina kasa na bawa banza ajiyar shi. Ya zauna Yana facing Dina, Amma se yayi shiru ya gagara yin magana balle ni da ko kallon inda take ma banyi ba, na Mike Dan na fita na bar Masa dakin, bazan iya cigaba da kallon shi ba, ganin shi kawai zuciyata zafi take min, for some unknown reason se nake jin he doesn't worth me. " They're planning to get you married, kin sani ko? Ya zamuyi ?" Na ji muryar shi me cikeda rauni ta daki kunnena, na juyo na kalleshi he looks so pitiful, kallon shi kawai seda ya raunana zuciyata, na dauke Kai nace " And so? Meye naka na auren da zaayi min? Ni kaina Ina mamakin dalilin da yasa na fara sonka, bansan har me na gani a tattare da Kai da yasa na soka ba..." " AFIYYA!..." Ya Kira da karfi tare da mikewa tsaye, Nima na katse shi da fadin " Kar ka min ihu! Bari na Gaya maka you don't worth aurena, nayi tunanin duk inda zaaje ba zakaji tsoron ka fito kayi defending Dina Amma jiya se Naga akasin hakan, se ka kasa cewa gurin ka nake zuwa, akanka na jure abubuwa da dama Amma Kai ka kasa Kare ni a wajen iyayenka, Kai kuwa me zaka iya yimin idan na aureka" " Afeey please kizo mu gudu, I can't imagine you with another guy..." Ya ciji leben shi idanun shi sunyi jawur yace " Zan Kira uncle Babawo right away na fada Masa halin da ake ciki" Ya fada Yana Ciro wayar shi daga pocket din pants din dake jikin shi na tracksuit, na karbe wayar nace " Don't blow up the matter so quickly Dude! Beside ni bana tunanin tunda iyayen ka Suka dage se sunyi min aure akwai Wanda ya Isa ya hanasu. Na mafi so su cigaba da daukar alhakina yadda Ina kallo zasu Shiga jahannama.." Hannun shi ya daga a zafafe zai mareni na tsaya cak nace " Mari? Mare ni Yaya,ai abinda ka koya kenan, sannan Dan Allah zo ka fita kafin mahaifiyar ka ta dawo tace na maka fyade!" Ya kalleni idanun shi kamar zasu fito Dan mamakin maganganu na sannan ga bacin ran halin da muke ciki. Yana fita na saki kuka a hankali Ina rike kirjina dake barazanar konewa saboda zafin da nake ji, na Jima Ina kuka sannan na Mike na Ciro tab dita nayi connecting na Kira Rooks, kamar tana jira tayi picking fuskar ta dauke da murmushi tace " Afeey darling!" Na Dan saki faint murmushi nace " Rooks darling! Ina Mummy da Abbah?" " Wait me ya sameki, Afeey marinki akai? Me ya sameki?" Na saki kuka da nake ta rikewa na fara fada Mata dukkan abinda ya faru, tayi shiru har na gama sannan tace " Afeey bazan iya rike wannan secret din ba, I've to inform Mummy. Ta Yaya Zaki cigaba da rayuwa a Haka? Afeey Mari ? Ciki? Shege shi Kuma yayan dama I never like your relationship wallahi! Kinsan ko kin aure shi kina tareda su Kawu Sa'idu, kinyi aure Amma zaa cigaba da rayuwar da akeyi, Allah ya hada kowa da rabon shi, don't feel bad Dan Kun rabu better days are coming" Cikin kuka nace " Se yaushe? Yaushe ne better days din? Yau ko gobe? Na gaji Rooks Ina jin kamar kaddarar ta yimin nauyi" Se ta fara kuka tana fada min nayi hakuri Allah Yana sane Dani, a karshe tace Dole zata fadawa Mummyb, Ta fada tana share hawayen dake bin fuskarta, na girgiza Kai nace " Baki gane ba Rooks, da Mummy dasu Kawu Tijjani suna da maganin yimin da tuni wani zancen ake ba wannan ba, tunda kiga Ina Shan wahala to tabbas Haka Allah ya tsara min, idan kin fada musu tada musu da hanakali kawai zakiyi, Dan hakan Dan Allah kiyi shiru, kema na fada Miki ne Dan naji sanyi a cikin raina. To Baki sani ba Rooks, Kawu sure zai min, karki fadawa kowa" " Da wa?" Na girgiza Kai alamun ban sani ba tace " Auren Dole AFIYYA? you mean Kawu zai maki aure da wanda Baki sani ba? Baki taba haduwa dashi ba? come on AFIYYA this is freaking 21st cent not lokacin da, rayuwa ta canja Afeey!" Nayi shiru Ina tunanin me zance ma Rooks dake bambami cikin wayar, abinda take bazai canja fact that aure kawu zai min ba, banida Wanda zai taimaka min. Da gaske na fahimci a wañnan lokacin zumunci ya Kare, lokacin da Abbu keda Rai ban taba kawowa watarana Zan tsinci kaina cikin wannan halin ba, ban taba kawowa ni wadda nake da gata Zan Kare a Haka ba, tabbas rayuwa zancen banza ce. " Come on Rooks, maganar nan ta tsaya tsakanin mu, bana son kowa ya sani, saboda Kawu Sa'idu yace zai fadawa kowa ni nake son mijin. do this for me sister please" Tayi shiru se can tace " Afeey are you ok? Are you sure Zaki iya hakan?" Na gyada Mata Kai inajin yadda zuciyata ke tarwatse wa tana bajewa and I was left shattered Amma dukda Haka Ina da yakinin Allah zai kawo min dauki! "But know that I'll always be there for you?" nayi murmushi daya fitar da dimples Dina Wanda ko magana nake lotsawa suke, I remembered Ummaan su na yawan cewa Yunwa CE tasa nake da dimple ba kyau ba. Auren ma nayi tunanin zaa hadani da Wanda Zan kalla naji dadi Amma da aka tashi se aka Nemo Wanda ko a lahira bana zata Masa Shiga aljanna, Kar kuga laifina Manzon Allah SAW yace Wanda yabi iyayenshi kamar ya bini ne, idan ka Saba musu ni ka sabawa! Shi yayi fatali da wannan maganar. Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment to 09063467258.28 Komai se nake ganin shi tamkar almara, cikin kankanin lokaci Kawu yayi blowing magana zuwa sauran Yan uwan shi uku. I was so naive then, I was so young then ko addua ba sosae nake ba gaba daya banyi understanding concept of kaddara ba, saboda Gani nake kawai duk abinda ya faru da Kai kawai kaddara ce and nothing, absolutely nothing will change kaddarar. Haka nan na Hana Rooks t fadawa kowa saboda Ina ganin Dole na karba dukkan abinda yazo cikin rayuwata. Yammacin jumaa Ina kwance se naji sallamar Kawu Sa'idu, bama sallama zance ba kwala min Kira kawai yake Yi, nayi saurin mikewa na dauki hijabi na na fito Yana tsaye a kofar dakin har na kusan yin Karo dashi, na Dan ja baya nace " Kawu Ina wuni?' Ya dalla min harara yace " Ki canja Kaya kizo mijinki yazo" Idanuna a warwaje nace " Miji Kuma?" Nayi saurin janyewa baya saboda dukan da ya kawo min, komawa nayi ciki Ina tausar zuciyata, Dan na riga na sawa zuciyata I'm accepting aurennan, da dai in cigaba da Zama gidannan to gwara na aura ko waye, bansan fadar hakan kuskure bane babba. Skirt da riga na saka, na kalla kaina Anty Nafisa matar uncle Babawo ita ta dinka min zuwanta na karshe Nigeria, ita kadai tazo wani biki shi ne tazo taga yadda nake. Yayi min cif cif, na fara budewa ta kasa, dukda shekaru na basuda yawa Amma Kuma Babu laifi jikina me kyau ne. Mayafin kayan na dakko na yafa na fito, Ummaan su na zaune ta kalleni ta kyabe Baki, bance komai ba na nufi waje wata kyakyawar 307 sabuwa dal se sheki take da daukar idanu baka wuluk. Yaya na tsaye ya hade Rai, na kalleshi shima tunda na fito idanun shi akai na yake, fuskar shi tana kunshe da tashin hankalin da kana kallon shi za ka iya karantawa, se Naga yayi rama a rabuwar da mukai shekaran jiya, tun da muka Gama wannan maganar ban Kara ganin Shiba. shida Baba da Kawu Sa'idu suna tsaye se wasu Baki Wanda nake tunanin daya daga cikin su shi Zan aura Yana tsaye , na karasa na gaishe su, dukkan su idanun su a kaina Kawu yace " Tsayuwar me kike ba Zaki karaso ba" Na tako a hankali har nazo dab dasu idanuna a kasa, ya dube ni yace " JUNAIDU se kayi hakuri, Haka take kamar Yar kauye, gata nan!" JUNAIDU na nanata cikin zuciyata, na daga idanuna na kalle su dukkan su shekarun su baya wuce talatin ba, sun Sha bugaggun shaddodin su, daya ruwan sararin samaniya dayan Kuma ruwan toka, dukkan si babu me hula a Kan shi and I wonder yadda banji Kawu yayi korafi ba, na tuna zuwan mijin Siyama na farko Bai zo da hula ba aka ta ciccira maganar se gashi wannan ma yazo a hakan. Tarkata yaran shi yayi Suka shige ciki ya barni tsaye Ina Wasa da hannuna cikin mayafi, " To Bari na Shiga mota se kuyi magana" Dayan ya fada Wanda ya tabbatar min da bashi bane Junaidun, ya wuce cikin motar, na dago na kalle shi he's handsome wannan shi ne abinda na fara fahimta Bayan kallon fuskar shi, he looks decent daga fuskar shi zaka fahimci baya da magana, he looks innocent and good. Wannan shi ake cewa illusion, what the eyes sees is not always real! To wannan shi ne abinda nayi idan ka kalle shi ba zaka taba tunanin he's thug ba, shi da halayen da yake exhibiting sunyi hannun riga, he appears a good man. Ganin yayi shiru Bai ce komai ba yasa na gaishe shi a karo na biyu, ya kalleni ya ce " Lafiya!" Ban Kara magana ba naji Raina na kokarin baci, a Haka nayi ta tsaye wajen minti talatin Dan hakan na Kara duban shi nace " Allah ya kiyaye hanya nagode!" Ban jira amsar shi ba na wuce cikin gida, Ina jin kaina ya cunkushe da tambayoyi iri iri sede Babu Wanda Zan iya amsawa a ciki Dan ni na bansan amsar ba, Babu Wanda na samu tsakar gida Dan haka na wuce daki na kwanta na lumshe idanuna Ina adduar Allah ya zaba mafi alkhairi. Bayan ishai Suka fita Ummaan su day Kawu se ya rage no kadai Dan Hafsa anyi hutu ta tafi Kano, Ina nan a kwance naji sallamar Yaya, da sauri na Mike Ian bin shi da kallo har ya samu guri ya zauna, na tsare shi da idanu Ina jin yadda ake min tickling a cikina, gaba daya naji farin ciki ya lullubeni, hakan ya Bata min rai kenan har yanzun Ina son shi. " Seems kamar kin yadda da wannan auren da zaayi Miki ko?" Nace " Eh!" Da mamaki ya kalleni yace " Bakya Sona kenan? Kin manta munyi alkawarin zamuyi Aire" Na mishi banza saboda gaba daya nema yake ya fitar min da nutsuwar da na fara samu, ganin nayi mishi shiru se ya Mike ya fita. A hankali na Kai hannuna na rike kirjina dake min zafi,nidai ban cancanci wannan rayuwar ba! " Me yasa kaki Mata magana?" Safiyyu ya tambaye shi lokacin da suka dauki hanya, Junaidu yace " Me zance Mata, nifa kaina mamakin yadda akai na yadda Zan aureta nake" Safiyyu yayi dariya yace " Nasan Mata basa gabanka Amma yarinyar nan karama ce Bata San komai ba , Dan Allah ka rike ta da kyau" Junaidu ya kalleshi Yana sakin dariya yace "Kai da bakin ka kake hadani da Allah?" Ya Kara kwashewa dariya yace " Kai kanka kasan badan an bani saa da aurenta ba Banga dalilin da zaisa na aureta ba, Kuma bayan Haka nafi son ta shigo da Shirin cewar uwarta zataci ba Dadi zata ji ba" Safiyyu yace " Tayi kankanta yarinyar, baka ganin kamar shima Sa'idun Yana da wani dalili na aura maka ita" " Eh mana dama ban Gaya maka ba? Yarinyar nada dukiya wadda take hannun kannenshi, yasan idan ya bar yarinyar tayi karatu watarana zata karbi dukiyar ta shiyasa ya hanata karatu, sannan ya aura min ita, to shi Malam na Dan Issa ya fada Masa idan ya aura min ita Babu jimawa dukiyar zata dawo hannun shi, ni Kuma idan na aureta zata zame min kariya daga dukkan sharri, sannan gidan mu da nake son ya tarwatse to zai tarwatse" Safiyyu ya jinjina Kai yace " Akwai samu kenan! Amma dukda Haka banso a saka yarinyar a ciki ba" Kamar yadda nayi tunani, washegari Sega Mummy da yamma itada Rooks, Kawu Tijjani ma ya iso. Ina daki na zubawa kayana Dana wanke idanu Amma ko daya na kasa ninkewa naji sallamar Mummy, nayi saurin sakin hular hannuna na mike, fuskarta dauke da murmushi ta rungume ni, Nima na rungume ta inajin sanyi cikin raina, ta sakeni ta zauna Nima na zauna se Kuma na dauki hijabi na fita Ina kallon Rooks da taki kallona, nayi murmushi na je wani shop kusa damu na siyo ruwa na dawo, Ina Zama Rooks ta matso nace Mata " Ni nayi fushi!". Mummy tana Mana dariya har muka fara Hira, na dubi Mummy nace " Yanzun na bayar a siyo awara abincin ya Kare" Tayi min murmushi yace " To daughter, kawun ki yace min kin fitar da miji ko?" Na danyi Murmushin yake na tuna kashedin da yayi min yau da safe akan kowa yazo nace ni nake son Junaidu ni na zabe shi, anan yake fada min shi din Dan kazaure ne. Na gyada Kai Ina sunkuyar da kaina , tayi murmushi tace " Amma jikina na bani you were forced. Tell me Afiyya gaskiyar magana" Na dago na kalla Rooks da ta ke Wasa da zoben hannunta Wanda take nuna nervousness dinta, nace " Mummy da gaske!" Se tayi murmushi again tace " Amma shi ne baki fada Mana ba, se saura sati biyu yake fada Mana. Allah ya Sanya alkhairi Amma naso ace ba aure Kika zaba ba karatu Kika zaba, dukda auren ma is in line, But tunda Haka ne ki sani Ina tare da Ke duk abinda kike so ki fadamin" Na Share hawayen idanuna nace " Mummy nagode!" Aka kawo awara tana ta min nasiha da guda min yadda zamantakewar aure take, se yamma Suka tafi Kawu yace na bisu saboda Shirin biki. Kwana biyu duk yadda nake son aiki ta hananin se hutawa kawai da nake tace nayi Rama da yawa kullum girki take koya min tana bani nutritious food Ina ci, ban Kara ji daga gurin angon ba, tunda ba waya ce Dani ba Dan ta gurin Yaya Shehu Kawu ya karba tun kafin na hada ta. Mummy ta Kira Nanny se gata ta taho ta fara guarani, nayi yar kiba nayi kyau. Da daddare tana mulka min wani yellow abu me azabar kamshi a jikina Rooks na zaune tana mitar se an shafa Mata tace " Ku fada min gaskiya meye zancen aurennan?" Nayi kirikiri nace " Ai na fada Miki ni na fito dashi" Tayi dariya kawai tace " Yara kenan!" Shirye shirye sosae Mummy keyi,saura sati daya Ina zaune a daki na hada kaina da gwiwa nayi shiru Kuma ni ba kuka nake ba Rooks ta zauna gefena tace " Afeey yanzun auren zakiyi? Wanda Baki taba sani ba shi Zaki zauna dashi, Afeey Ina jin kamar I'm a bad person da nake kallo kina Shan wahala Amma na kasa fadawa kowa" Na riko hannunta nace " Watarana zanji Dadi karki damu" A wañnan Daren Ummiey ta iso da family dinta, Haka Uncle Babawo Wanda min ringa munyi waya a wayar Mummy. Ummiey na yin wankan ta taho gidan Mummy ta same ni a parlor ana turara ni, Mummy nata duba kayan kitchen din da tayi order. Ummiey ta zauna Suka gaisa, Suka gaisa da Nanny " Yanzun Maryam yarinyar nan tayi kankanta da aure shekara Sha biyar fa!" Mummy ta sauke ajiyar zuciya tana kallona tace " To ya zanyi? Ita ke son shi, da farko nayi tunanin Yaya Sa'idu ke fada kawai Amma ta tabbatar min da bakinta Haka ne" Ta girgiza Kai tace " To Allah ya Sanya alkhairi, shi Kinga mijin anyi bincike sosae" Mummy tacr " Munyi maganar da Sa'idu yace komai steady Kuma Wai baya gari shiyasa Bai zo min gaisa ba" Itadai Ummiey kawai kanta take gyadawa Amma dukda Haka idan muka hada Ido se nayi saurin sauke idanuna Dan gani nake she's seeing through me. AFIYYA is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment through 0806346725828 Komai se nake ganin shi tamkar almara, cikin kankanin lokaci Kawu yayi blowing magana zuwa sauran Yan uwan shi uku. I was so naive then, I was so young then ko addua ba sosae nake ba gaba daya banyi understanding concept of kaddara ba, saboda Gani nake kawai duk abinda ya faru da Kai kawai kaddara ce and nothing, absolutely nothing will change kaddarar. Haka nan na Hana Rooks t fadawa kowa saboda Ina ganin Dole na karba dukkan abinda yazo cikin rayuwata. Yammacin jumaa Ina kwance se naji sallamar Kawu Sa'idu, bama sallama zance ba kwala min Kira kawai yake Yi, nayi saurin mikewa na dauki hijabi na na fito Yana tsaye a kofar dakin har na kusan yin Karo dashi, na Dan ja baya nace " Kawu Ina wuni?' Ya dalla min harara yace " Ki canja Kaya kizo mijinki yazo" Idanuna a warwaje nace " Miji Kuma?" Nayi saurin janyewa baya saboda dukan da ya kawo min, komawa nayi ciki Ina tausar zuciyata, Dan na riga na sawa zuciyata I'm accepting aurennan, da dai in cigaba da Zama gidannan to gwara na aura ko waye, bansan fadar hakan kuskure bane babba. Skirt da riga na saka, na kalla kaina Anty Nafisa matar uncle Babawo ita ta dinka min zuwanta na karshe Nigeria, ita kadai tazo wani biki shi ne tazo taga yadda nake. Yayi min cif cif, na fara budewa ta kasa, dukda shekaru na basuda yawa Amma Kuma Babu laifi jikina me kyau ne. Mayafin kayan na dakko na yafa na fito, Ummaan su na zaune ta kalleni ta kyabe Baki, bance komai ba na nufi waje wata kyakyawar 307 sabuwa dal se sheki take da daukar idanu baka wuluk. Yaya na tsaye ya hade Rai, na kalleshi shima tunda na fito idanun shi akai na yake, fuskar shi tana kunshe da tashin hankalin da kana kallon shi za ka iya karantawa, se Naga yayi rama a rabuwar da mukai shekaran jiya, tun da muka Gama wannan maganar ban Kara ganin Shiba. shida Baba da Kawu Sa'idu suna tsaye se wasu Baki Wanda nake tunanin daya daga cikin su shi Zan aura Yana tsaye , na karasa na gaishe su, dukkan su idanun su a kaina Kawu yace " Tsayuwar me kike ba Zaki karaso ba" Na tako a hankali har nazo dab dasu idanuna a kasa, ya dube ni yace " JUNAIDU se kayi hakuri, Haka take kamar Yar kauye, gata nan!" JUNAIDU na nanata cikin zuciyata, na daga idanuna na kalle su dukkan su shekarun su baya wuce talatin ba, sun Sha bugaggun shaddodin su, daya ruwan sararin samaniya dayan Kuma ruwan toka, dukkan si babu me hula a Kan shi and I wonder yadda banji Kawu yayi korafi ba, na tuna zuwan mijin Siyama na farko Bai zo da hula ba aka ta ciccira maganar se gashi wannan ma yazo a hakan. Tarkata yaran shi yayi Suka shige ciki ya barni tsaye Ina Wasa da hannuna cikin mayafi, " To Bari na Shiga mota se kuyi magana" Dayan ya fada Wanda ya tabbatar min da bashi bane Junaidun, ya wuce cikin motar, na dago na kalle shi he's handsome wannan shi ne abinda na fara fahimta Bayan kallon fuskar shi, he looks decent daga fuskar shi zaka fahimci baya da magana, he looks innocent and good. Wannan shi ake cewa illusion, what the eyes sees is not always real! To wannan shi ne abinda nayi idan ka kalle shi ba zaka taba tunanin he's thug ba, shi da halayen da yake exhibiting sunyi hannun riga, he appears a good man. Ganin yayi shiru Bai ce komai ba yasa na gaishe shi a karo na biyu, ya kalleni ya ce " Lafiya!" Ban Kara magana ba naji Raina na kokarin baci, a Haka nayi ta tsaye wajen minti talatin Dan hakan na Kara duban shi nace " Allah ya kiyaye hanya nagode!" Ban jira amsar shi ba na wuce cikin gida, Ina jin kaina ya cunkushe da tambayoyi iri iri sede Babu Wanda Zan iya amsawa a ciki Dan ni na bansan amsar ba, Babu Wanda na samu tsakar gida Dan haka na wuce daki na kwanta na lumshe idanuna Ina adduar Allah ya zaba mafi alkhairi. Bayan ishai Suka fita Ummaan su day Kawu se ya rage no kadai Dan Hafsa anyi hutu ta tafi Kano, Ina nan a kwance naji sallamar Yaya, da sauri na Mike Ian bin shi da kallo har ya samu guri ya zauna, na tsare shi da idanu Ina jin yadda ake min tickling a cikina, gaba daya naji farin ciki ya lullubeni, hakan ya Bata min rai kenan har yanzun Ina son shi. " Seems kamar kin yadda da wannan auren da zaayi Miki ko?" Nace " Eh!" Da mamaki ya kalleni yace " Bakya Sona kenan? Kin manta munyi alkawarin zamuyi Aire" Na mishi banza saboda gaba daya nema yake ya fitar min da nutsuwar da na fara samu, ganin nayi mishi shiru se ya Mike ya fita. A hankali na Kai hannuna na rike kirjina dake min zafi,nidai ban cancanci wannan rayuwar ba! " Me yasa kaki Mata magana?" Safiyyu ya tambaye shi lokacin da suka dauki hanya, Junaidu yace " Me zance Mata, nifa kaina mamakin yadda akai na yadda Zan aureta nake" Safiyyu yayi dariya yace " Nasan Mata basa gabanka Amma yarinyar nan karama ce Bata San komai ba , Dan Allah ka rike ta da kyau" Junaidu ya kalleshi Yana sakin dariya yace "Kai da bakin ka kake hadani da Allah?" Ya Kara kwashewa dariya yace " Kai kanka kasan badan an bani saa da aurenta ba Banga dalilin da zaisa na aureta ba, Kuma bayan Haka nafi son ta shigo da Shirin cewar uwarta zataci ba Dadi zata ji ba" Safiyyu yace " Tayi kankanta yarinyar, baka ganin kamar shima Sa'idun Yana da wani dalili na aura maka ita" " Eh mana dama ban Gaya maka ba? Yarinyar nada dukiya wadda take hannun kannenshi, yasan idan ya bar yarinyar tayi karatu watarana zata karbi dukiyar ta shiyasa ya hanata karatu, sannan ya aura min ita, to shi Malam na Dan Issa ya fada Masa idan ya aura min ita Babu jimawa dukiyar zata dawo hannun shi, ni Kuma idan na aureta zata zame min kariya daga dukkan sharri, sannan gidan mu da nake son ya tarwatse to zai tarwatse" Safiyyu ya jinjina Kai yace " Akwai samu kenan! Amma dukda Haka banso a saka yarinyar a ciki ba" Kamar yadda nayi tunani, washegari Sega Mummy da yamma itada Rooks, Kawu Tijjani ma ya iso. Ina daki na zubawa kayana Dana wanke idanu Amma ko daya na kasa ninkewa naji sallamar Mummy, nayi saurin sakin hular hannuna na mike, fuskarta dauke da murmushi ta rungume ni, Nima na rungume ta inajin sanyi cikin raina, ta sakeni ta zauna Nima na zauna se Kuma na dauki hijabi na fita Ina kallon Rooks da taki kallona, nayi murmushi na je wani shop kusa damu na siyo ruwa na dawo, Ina Zama Rooks ta matso nace Mata " Ni nayi fushi!". Mummy tana Mana dariya har muka fara Hira, na dubi Mummy nace " Yanzun na bayar a siyo awara abincin ya Kare" Tayi min murmushi yace " To daughter, kawun ki yace min kin fitar da miji ko?" Na danyi Murmushin yake na tuna kashedin da yayi min yau da safe akan kowa yazo nace ni nake son Junaidu ni na zabe shi, anan yake fada min shi din Dan kazaure ne. Na gyada Kai Ina sunkuyar da kaina , tayi murmushi tace " Amma jikina na bani you were forced. Tell me Afiyya gaskiyar magana" Na dago na kalla Rooks da ta ke Wasa da zoben hannunta Wanda take nuna nervousness dinta, nace " Mummy da gaske!" Se tayi murmushi again tace " Amma shi ne baki fada Mana ba, se saura sati biyu yake fada Mana. Allah ya Sanya alkhairi Amma naso ace ba aure Kika zaba ba karatu Kika zaba, dukda auren ma is in line, But tunda Haka ne ki sani Ina tare da Ke duk abinda kike so ki fadamin" Na Share hawayen idanuna nace " Mummy nagode!" Aka kawo awara tana ta min nasiha da guda min yadda zamantakewar aure take, se yamma Suka tafi Kawu yace na bisu saboda Shirin biki. Kwana biyu duk yadda nake son aiki ta hananin se hutawa kawai da nake tace nayi Rama da yawa kullum girki take koya min tana bani nutritious food Ina ci, ban Kara ji daga gurin angon ba, tunda ba waya ce Dani ba Dan ta gurin Yaya Shehu Kawu ya karba tun kafin na hada ta. Mummy ta Kira Nanny se gata ta taho ta fara guarani, nayi yar kiba nayi kyau. Da daddare tana mulka min wani yellow abu me azabar kamshi a jikina Rooks na zaune tana mitar se an shafa Mata tace " Ku fada min gaskiya meye zancen aurennan?" Nayi kirikiri nace " Ai na fada Miki ni na fito dashi" Tayi dariya kawai tace " Yara kenan!" Shirye shirye sosae Mummy keyi,saura sati daya Ina zaune a daki na hada kaina da gwiwa nayi shiru Kuma ni ba kuka nake ba Rooks ta zauna gefena tace " Afeey yanzun auren zakiyi? Wanda Baki taba sani ba shi Zaki zauna dashi, Afeey Ina jin kamar I'm a bad person da nake kallo kina Shan wahala Amma na kasa fadawa kowa" Na riko hannunta nace " Watarana zanji Dadi karki damu" A wañnan Daren Ummiey ta iso da family dinta, Haka Uncle Babawo Wanda min ringa munyi waya a wayar Mummy. Ummiey na yin wankan ta taho gidan Mummy ta same ni a parlor ana turara ni, Mummy nata duba kayan kitchen din da tayi order. Ummiey ta zauna Suka gaisa, Suka gaisa da Nanny " Yanzun Maryam yarinyar nan tayi kankanta da aure shekara Sha biyar fa!" Mummy ta sauke ajiyar zuciya tana kallona tace " To ya zanyi? Ita ke son shi, da farko nayi tunanin Yaya Sa'idu ke fada kawai Amma ta tabbatar min da bakinta Haka ne" Ta girgiza Kai tace " To Allah ya Sanya alkhairi, shi Kinga mijin anyi bincike sosae" Mummy tacr " Munyi maganar da Sa'idu yace komai steady Kuma Wai baya gari shiyasa Bai zo min gaisa ba" Itadai Ummiey kawai kanta take gyadawa Amma dukda Haka idan muka hada Ido se nayi saurin sauke idanuna Dan gani nake she's seeing through me. AFIYYA is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment through 08063467258..29 " Ummiey tun tuni nace Miki Ina sonta Zan aureta, Ummiey Kika ki yadda! Ummiey gashi ina kallo a young age din nata zaayi Mata aure and I'm sure Bata son mijin!" Ummiey ta dafe kanta, wannan dalilin ta so ace Shehu Bai biyo ta ba, Amma tunda yaji labarin aurennan gaba daya nutsuwar shi ta tafi, ita gani take kamar Wanda yake nema ya zautu. " Me ka sani Shehu? Afiyya da kanta ta zaba mijinta, da bakinta race min ita tace tana son shi..." Shehu ya Kara Shiga damuwa yace " Se kuka yarda da ita Ummiey? Kina ganin gaskiyaa ta Fadi maki? That girl has already giving up! Ko Baku lura ba Ummiey? Ta riga ta cire tsamannni daga afuwar rayuwa, tana ganin rayuwa ba wajen da zaka samu sauki bane Ummiey! Why are you all blind Ummiey, ta Yaya zaku barta tayi ta Shan wahala a hannun wancan azaalumin..." " Shehu!" Ummiey ta daka Masa tsawa, ya dago idanun shi da sukai ja ya dubi Ummiey da take kallon shi a bace " Ya zanyi? Shehu Yan uwan babanta ne, shi ne marikin ta Shehu. Ya zanyi Kuma banida wani kwakwaran shaidar cewar auren Dole ne, Afiyya tayi testifying cewar ita take son shi. What else do you want me to do!" " Duk laifin ku ne Ummiey, da Kun riketa da kyau Kun jata a jiki how'll that animal in human form zai dinga wahalar da ita" Yana Gama fadar haka ya saka kanshi ya bar parlon ya bar Ummiey zaune da tagumi. Sarki ya karaso ciki ya zauna gefen Ummiey sede baiyi magana ba " Na sani munyi kuskure babba, min watsar da Yar Halima. Halima ta fiye min dukkan Yan uwana Amma bansan me yasa da ta rasu na kasa daukar Yar ta ba, bansan me yasa na dinga fushi da ita ba, I never imagined Yar Halima cikin wannan mess din. Sarki I'm a bad sister" Ta fada tana riko hannun shi, ya gyada kanshi yace " Haka ne Ummiey, the worst thing shi ne babu lokacin gyara, lokaci ya rigada ya Kure" Se ta fara kuka tana Kara kankame hannun shi cikin nata. Babu jimawa se ga Yaya Shehu ya karaso gidan Mummy. Ina can bedroom din Mummy Ina Shan fruit, nayi kyau jikina yayi kyau se glowing yake irin na asalin amaren nan, ko raba ta kazo Yi zakaji kamshi me dadi dake tashi daga jikina, tabbas idan da ace Wanda na aura mutumin arziki ne ko Kuma ace dukkan mu muna son juna to Babu tantama da yayi saa, Nanny tayi kokari sosae. Duk wannan abin da ake Yi Kuma Banda Rama Babu abinda nake Kara Yi, Rooks dake zaune tana kallona yadda nayi shiru very deep in thought, I'm very stupid I know Amma Nima baa wannan lokacin nasan I was stupid din ba se daga baya idan na tuna abubuwan da Kuma shirmen da duk nayi se naji haushin kaina nake ji, naji Ina tuhumar kaina da rashin trusting Allah, da Kuma rashin trusting rayuwa, Dan da ace nayi trusting din rayuwa na Kuma game menene concept na kaddara I would have prayed. But I was so reluctant, na saka a raina Babu inda sauki zai zo, na sawa Raina duniya ba gurin jin Dadi bace na Kuma saka a raina Babu me zuwa kawo min dauki. " Keeee tunanin me kikeyi Haka?" Rooks ta tambaya tana bubbuga kafada ta, na girgiza Kai Ina sakin fork din hannuna cikin bowl din nace " Ba komai, just some few thoughts!" Tayi murmushi tace " Ina Miki fatan alkhairi Afiyya,ke Kuma path din da Zaki bi kenan Haka Allah ya tsara Miki. Make this relationship work, ki bashi hadin Kai Allah kadai yasan me ya tanada Miki a ciki" Nayi murmushi kafin nayi magana naki muryar Nanny na Kirana, nayi saurin saka hijabi na fito, ta dubeni tace min naje Mummy na Kirana a parlon kasa. Cikin nutsuwa na dinga tattaka stairs har na sauka kasa, na nufi parlon da Babu kowa a ciki, idanuna cigaba da cillawa se da nazo tsakiyar parlon sannan na lura da Yaya Shehu dake zaune ya hada kanshi da gwiwa, nayi saurin Zama Dan nesa dashi nace " Yaya!" Da sauri ya dago idanun shi ya sauke kaina, cikin sauri na kawar da nawa saboda yadda sukai jawur, ga Kuma bacin Rai da ya kwanta cikin idanun ya fito kurkuru. Cikin wata murya da take a hargitse kamar yadda shi dinma a hargitse yake, fuskar shi looks pale yace " Are you stupid?" Na kalleshi da mamaki idanuna a warwaje Amma ni din Afiyya ce indai wajen share mutum ne na Masa banza Ummaan su Yaya ma ta buga ta barni. " Bakiji tambaya nayi Miki ba? Kina haukana zakice ke Kika ce kina son a Miki aure? Come on Afiyya Baki ce min karatu kike so kiyi a Oxford University ba? Didn't I promise you to stand for you and make all your dreams true? What does it takes ki ce musu auren Dole zaayi miki, why are you doing this?" Nayi shiru dukkan kalmomin da take fada na dukan kunnena Haka hearing nerves Dina na dauka suna kaiwa kwalkwalwata tana interpreting Ina fahimtar me yake cewa. Na taba fada muku son da Yaya Shehu yake minis immeasurable? Ko ni bansan yawan son da yake min ba, bansan how much Zan fada muku irin son da take min ba, a wasu lokutan a rayuwar mu we always go for the wrong person kamar yadda Sofy tayi akan Alby dinta. " Afiyya kiyi hakuri just tell them wannan animal in human form dinne yayi forcing din ki, kinada chance Amina ki fada yadda zaa San abinyi" " Ni Ina son shi!" Na fada Ina kawar da kaina, I dunno why I was so adamant, I really don't know, Ina furta hakan Naga gaba daya jijiyoyin dake wuyan shi da kanshi Wanda Zan iya gani sun tashi,idanun shi ya runtse tare da naushi sofar da yake Kai ya furta " Damn it! See Afiyya, ba Dole se kin kula ni ba, ba Dole se kinyi reciprocating feelings Dina ba, Dan Allah ki Fadi gaskiya for once kiyi farin ciki cikin zuciyar ki, it's so obvious aurennan na Dole ne, duka shekaran ki nawa , yaushe Kika San meye so?" Yafi mintinann da bazan iya lissafawa ba Yana persuading da ni ba, Amma Haka na ki Koda cewa komai. Karshe na Mike na tafi na barshi a gurin , why did I done that? Nima bansani ba, kawai na koma kawai auren nake son ayimin. Na koma daki na dinga kuka Ina Jim zuciyata na yimin zafi, Haka na hakura Dan kaina. Da daddare Ina kundundune cikin blanket se naji sallamar Mummy da Uncle Babawo, na Yi saurin mikewa na zauna Ina kirkiro murmushi nace " Uncle" Ya zauna yace " Princess!" Se idanuna suka ciko da kwalla, Abbuna he always call me Princess, Allah ya rahmushe shi ya jikan shi har da Mama da dukkan musulmi. Mummy tafita hakan ya tabbatar min magana zamuyi , na gyara zamana yace " A Ina kuka hadu da wannan guy din Junaidu?" Wani gumi a take ya karyo min, na fara fidgeting da fingers dina, kana kallona kasan banida gaskiya, shi Kuma se Bina yakeda kallo, se can nace " I lied! Kawu ne yace na aureshi" " You ok with that? Wait meyasa kika mana karya in the first place?" Na share kaina nace " He threatened me, Dan Allah Uncle kayi hakuri da na muku karya bansan yadda zanyi ba" Ya danyi murmushi yace " I know we failed you, mu ba iyayen arziki bane, but Afiyya ya kamata duk halin da kike ciki ki fada Mana. Though na Kara bincike sede wasu sunce ba mutumin arziki bane wasu sun Fadi akasin hakan. So far Zan Kara bincike kafin zuwa asabar din. Ki dinga cin abinci" Se naji dadi har bansan hawaye ya sakko min ba, se naji wani hope yazowa zuciyata, har ma da ya fita se na kwanta na fara bacci cikin jin Dadi, sede cikin dare na farka maganganun Yaya Shehu suka tayimin echo a kaina se naji na damu sosae, naji fuskar shi da idanun shi sun kasa gushewa a idanuna. Shirye shiryen ya cigaba da tafiya ban Kara saka Yaya ko Yaya Shehu a idanuna ba se ranar saka lalle ko nace walima Dan a Ringim abinda Suka go kiranta dashi kenan. Da daddare Ina ciccire kayan jikina Nads tazo tace min nazo Yaya Shehu na Kirana, na saka hijab na nufi waje Ina jin kamar zanyi gudu saboda Ina son na ganshi na tabbatar da whether he's fine or not. Ina zuwa na samu Yan maiduguri aunties Dina sun zo, ana cewa a kirani mu gaisa, nayi saurin rufe fuskata na fita, dan nasan aka tsaya wannan formalities din bazan je ba. Kamar yadda ta cemin Yana parking space nan na tarar da motar shi, Yana hangoni ya bude min gaban seat dake gefen shi, Babu musu na Shiga na kulle, ai kuwa ya saka central lock ya datse sannan yayi reverse ya fita daga gidan a Dan guje, a tsorace nace "Ina zaka kaini? Me za Kai min?" Ba tareda ya kalleni ba yace " I'm eloping you! Dole se na Hana aurennan at any cost...." Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria. Send evidence of payment through 09063467258 Talla! ✌🏼Fitattu biyu masu ban mamaki🫀Hakika babban goro sai magogin ƙarfe 😍, Hakk'un wani kaya sai amale ke d'auka🐫, Fitattu biyu👯🏽‍♀sun shiirya tsaf domin nishad'antar daku 🤓 sun shirya tsaf domin fadakar daku🧠 sun shirya tsaf domin dilmiya zuciyoyin ku cikin bege da shauk'in so💋💞, wohoho tabbas ️sahun giwa👣 mai ɓadda na raƙumi 🐪,Fitattu biyu😍✌🏼 masu tafiyar k'asaita, sheƙi, da walwali hak'ik'a koda kud'in ka saida rabon ka😘🏃🏽‍♀️ Fitattun Ƙarshen shekara😍 salon su daban ne dana sauran domin natsuwa da tunani sunyi aiki pure love and romance abun dai sai wanda yakaranta😍 maza ku hanzarta neman naku karku bari abaku labari🏃🏽‍♀️ #Oum Sumayya:- *GAMIN GAMBIZA*✍🏽 Nrml 300 Vip 500 #Oum Ikram:- *SOYAYYA CE SILAH* ✍🏽 Nrml 300 Vip 500 Duka biyu 400👌🏼 Vip 700👌🏼 Via 4210014214 Eco bank and send the evidence of payment via 08139624956 Or mtn/airtel credit via 07017296839 banda vtu hoton kati kawai!30 " Eloping?!" Na mainaita Ina kallon shi da mamaki, Sam ba kallona yake ba hasalima hankalin shi na kan shi da dukkan hankalin shi suna Kan tukin da yake, " Me kike tunani? Kina tunanin son da nake Miki kadan ne? Ko Kuma tunanin ki Zan zuba idanu ayi Miki aure ba tareda son ranki ba, idan kikai wannan tunanin to ba kiyiwa son da nake Miki adalci ba" Na sauke ajiyar zuciya me nauyi, sure wannan Yana bashi babban matsayi cikin zuciyata ba tareda shi kan shi ko Nima na sani ba. " Yaya Shehu kasan duk abinda hakuri Bai bayar ba rashin shi bazai bayar ba, you can't just do this. Dan Allah ka maida ni gida" Ya maka min wata harara wadda nasan tsabar yadda ranshi ke bace ne yasa ba ma zai iya min magana ba. Na dauke kaina Amma zuciyata Taki aminta da Wai na gudu, why should I be a coward, I've to accept whatever comes my way! Zuciayata ta tuna min, se kuwa na fara kici kicin bude kofa dukda yayi locking duka kofofin, wannan kicinayar da nake Yi yasa hankalin shi ya dawo kaina gaba daya, har ya kasa controlling brakes din, se ji nayi " Gab!" Ya bugawa wani mota. Tuni na sake kofar Ina maida numfashi, yayi saurin parking ya fito, me motar shima ya riga da ya fito, tuni mutane suka fara taruwa Dan kallon abinda ya faru, ni dashi Banda mun saka seat belt da Babu abinda zai hana mu bugu. " Gimbiya wancan kamar motar Shehu nake gani?" Daddy ya fada Yana duban Ummiey dake amsa waya, tayi saurin kallon gurin tace " Subhannallah! Wallahi shi ne" Daddy yayi saurin parking ya fito, Ummiey ma haka, crossing titin sukai zuwa inda ake ta gutsitsira magana, Shehu na tsaye ya dafe Kan shi ni Kuma Ina cikin motar se zazzare idanu nake, gabana yayi mummunan faduwa ganin Ummiey da Daddy, na fara kokarin fita Amma babu halin hakan saboda yadda ko Ina yake a kulle, yasan Zan iya komawa gida shiyasa ya kulleni, baifi 30 minutes ba Naga mutane na ta tafiya daya Bayan daya,Ummiey na rike da hannun shi ya zura key ya bude motar, kaina a kansu nayi tsuru tsuru kamar kace fit in zura a guje, Ummiey da mamaki take kallon fuskata sannan ta kalla tashi, Daddy yace " Afiyya!" Nayi saurin sunkuyar da kaina kasa, Ummiey ta maida kanta Kan Daddy sannan ta dubi Yaya da yayi shiru yana Kara tamke fuska, cikin sanyin murya Ummiey tace " Shehu me kukeyi tare? Ina zaka kaita? Me na fada maka?" Ya bude baki zaiyi magana face " Oh please Shehu ka manta duk abinda na fada maka. AFIYYA fito!" Babu musu na fito Ina ta kallon shi he looks defeated and depressed, se naji kamar kada na tafi Amma iyayen shi dake gurin ba abokan musu na bane, bayan mota na kwantar da kaina Ina jin sanyi duka na bin jikina, I felt so empty and lost, na Jin tamkar anyi nesa Dani daga barin jikina. Cikin motar Babu Wanda yayi magana seda muka Isa gidan mummy sannan muka fito fuskata a rufe da hijabi kamar yadda nayi Dana fita, Babu Wanda ya lura Dani har na haura sama kamar yadda Ummiey tace min, na Shiga dakin na samu Mummy na fadin " Wai ya zaku ce Baku ganta ba, Afiyyan allura ce da zata Bata?" Nayi sallama jikina a sanyaye na shigo " Daga Ina kike?" Na dake nace " Yaya Shehu ne ya kirani waje" " Me yasa Zaki fita Baki fada min ba duk kin tayar min da hankali" Nanny ta dubeni da banma lura da ita ba tace " Karki Kara fita ko Ina" Na gyada kaina, wani sabon lace ta dakko min cikin katon akwatin da kayan da nake fitar biki suke ciki ta bani na saka, sun yimin cif cikin jikina, kudos to me dinkin, yasan aikin shi, sede dukda abubuwan da yasa da zasu Kara cikani, kallo na kawai zakai ka kalla zallar yarinta a tare dani, ga jikina ma kawai ka kalla will tell you my age. Haka muka fita Ina ta zuba kamshi akan kamshi, muka Isa babban parlon bakin ta, suna zaune sun kusa su biyar koma din hakan, kana kallonsu kasan Yan gayu ne Kuma a wadace suke, dukkan su Kama suke da Ummiey, Mamana da Kuma ni kaina Banda mutum biyu da nake tunanin ko su sirikai ne Dan su kamannin su daban ne da namu. Tsakiyar su Mummy ta aje ni dukkan su suka yo kaina kowa na kokarin hadani da jikin shi, a raina nace a banza tunda se yanzun sukai niyyar hakan, suka zo nemana, a daddare na gaishe su kowacce ta min introducing kanta, biyu daga ciki cousins din Mama ne, biyar sister's dinta se biyu in laws dinta, matan brothers dinta kenan. Babu jimawa Ummiey ta shigo, Suka sakani a gaba da wasu zantuka da Suka saka naji tamkar na zura saboda girman su day Kuma nauyin su a kunne na. Ya zanyi Mummy ko motsi nayi se ta Harare ni, Haka na baza kunnuwa Ina ji, suna gamawa kuwa na Mike na fice a guje. Anty Bintu tana dariya tace "Anty Maryam yarinyar ki kunyar auren ma take ji ai" Mummy ta tabe baki tace " Allah dai ya kyauta" Daga nan suka koma hirar nayi kankanta ace an biye min anyi min aure, Ummiey da Mummy sede su kalli juna kawai Amma Babu me bakin magana. A Haka washegari tayi Kamar yadda aka saka karfe Sha daya zaa daura min aure. Gidan ya cika sosae da mutane, mutanen da na dinga bukata duk Basu zo ba se yanzun Wai a Haka boye zancen auren akeyi Dan kada a zarge su da rashin kula Dani. Tun sassafe Kawu Tijjani yazo shida Kawu Sa'idu, sun Jima da mummy bansan me suke tattauna wa ba, Kawu Sa'idu ya fara tafiya sannan Kawu Tijjani, ta shigo dakin da nake an shirya ni fes cikin wani dakakken lilac lace me adon zare maroon, nayi kyau ba karya, na kalla kaina for an uncountable number and I wishes I was happy, lokaci na farko naji inama ace Yaya Shehu ne mijina, may be da tuni Ina nan Baki na kamar zai yage Dan farin ciki. Nayi mamakin duk shige da ficen da akeyi Babu Uncle Babawo, har na tambayi Anty Nafisa lokacin da ta saka ni a gaba da abinci, nace " Banga Uncle ba" Ta danyi murmushi tace " Tun shekaran jiya Yana kazaure, munyi waya dashi Yana Hanya" Nayi shiru Ina Wondering me ya kaishi Kazaure, ban dai ce komai ba na dauka spoon din na fara cin dambun shinkafar da nace zanci. Babu jimawa Sha daya ta doka aikuwa Babu ko Kara minti akan lokacin aka daura min aure ni da Junaidu, what a destiny, mutumin Dana gani sau daya, ban ma taba jin muryar shi ba, zuciyata tayi min nauyi Dole na sulale daga cikin cousins Dina Dan kawayena Babu Wanda yazo tun ranar walima hatta Sauda Bata Kara zuwa gurin bikin ba, daga ni se cousins dina su Rooks dasu Nads se Wanda sukazo daga Maid da ko Gama rike sunan su banyi ba. Ina nan naji gidan ya kacame da guda da Kuma kiraye kirayen isowar ango, da sauri nayi toilet na kulle kofar tareda jingina kaina jikin kofar, a hankali hawaye masu zafin gaske suka cigaba da sakkowa akan fuskata, na zauna dabar a saman tiles din da suke malale cikin bandakin bama na tsoron soiling kayana, kawai sanyi nake bukata, so nake na samu abinda zai saka min naji sanyi a jikina, na Jima Ina kuka seda naji zuciyata tayi dadi sannan na Kuma daina jin muryoyin mutane nasan ya fita, na saka wipes nayi wiping fuskata sannan na wanke na fito, Anty Bintu ce kadai dakin alamun jirana take, na saki Mata Murmushin karya, ta Bata Rai, ta fisu sakin fuska hakan yasa har na Saba da ita. " Me kike yi a toilet tun dazun har angon yazo ya tafi?" Na sauke ajiyar zuciya jin har ya tafi, nace " Bana jin Dadi" Se ta tashi ta riko ni ta fara fada min kowacce mace da Haka ta girma, ni nayi saa na zaba mijina, Amma Mamana rakiyar marriage alliance kawai tayi Bata dawo ba seda mijinta, ta min nasiha wadda tasa na Dan ji sanyi a raina sannan ta gyara min fuska na fita aka fara hotuna Dani. Yadda aka saka karfe uku zaa kaini saboda da Dan tazara tsakanin Ringim da Kazaure. An Gama shirya ni tsaf, a nada min lafayar da ta jiku da kamshi Sega Ummiey ta shigo tace ba yau zaa kaini ba, till further notice. Na dago Ina kallon ta da mamaki tace min nasa hijab nazo parlon Baban Rooks. Ina zuwa na samu Uncle Babawo Yana fadin " Na hadu da babanka Kuma ya fada min halayen ka Dan hakan se ka saki yarinyar nan, seda nace a jira na dawo Amma aka daura. Kaji tsoron Allah Sa'idu idan Yar kace ai ba zaka nata Haka ba" Duk shi kadai yake maganar, Mummy na gefe se ruwan hawaye take yayinda Kawu Sa'idu yayi fitinfitin akan aure an daura Babu Wanda ya Isa yasa a kunce. Daddy a nutse yace " Kai Junaidu mahaifinka da bakin shi yace ya Kore ka saboda kana bin bokaye, Yan unguwa sunce baka ma zuwa sallah baa taba ganinka a masallaci ba, kaga baka cancanci Afiyya ba, Dan hakan ga takadda da biro ka rubuta Mata sakin ta duk abinda ka kashe no Zan biyaka" Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam, First bank of Nigeria. Send evidence of payment to 0906346725831 Wani irin kallo yake bin dukkanin su dashi, se a lokacin kamanin shi da yake boyewa suka fito, tabbas he doesn't look any thing near innocent person, yafi Kama da takkadiran marasa mutunci, a idanun shi kawai Dana kalla naji wani irin tsoron shi ya darsar min cikin zuciya ta, nayi saurin sunkuyar da kaina Ina jin yadda gabana yake wani irin faduwa. Ban karasa ciki ba saboda yadda ake tafka rigima, Dan tun suna maganar a hankali har ta koma kowa jijiyar wuyan shi ta mike, su sunce lallai lallai Babu inda zanje se ya sakeni Dan bazasu hada zuria da irin shi ba yayinda shi Kuma ya dage ba zai sake ni ba, da kowanne yayi insisting akan maganar shi se kawai Junaidu ya mike, duka Suka bishi da kallo Babu wata wata yayo kaina, Bai jira komai ba ya daukeni cilak tamkar wata teddy ya Saba a kafadar shi ya fita, Kawu Sa'idu yayi saurin Mara Masa baya Yana fadin hukuncin da yayi ya burge shi, Haka Ina doka hannu Wana a bayanshi, kafafuna Ina ta hantsila su Wanda ko takalmi Babu amma ko gezau baiyi ba seda ya direni cikin wata bakar Corolla LE sannan ya maida murfin ya rufe, glasses din tinted ne Babu Wanda ke kallona, Amma ni Ina kallon yadda suke magana kasa kasa shi da Kawu Sa'idu, Basu dauki lokaci ba Sega sauran mazauna parlon sun fito, Uncle Babawo da Daddy suka nufo gurin Amma kafin su karaso tuni ya shaiga motar yaja uban reverse yayi Kan titi, na saki matsanancin kuka, a lokacin ji nake tamkar rayuwata ta Kare, tamkar Babu wani farin ciki da yayi saura, Banda gudu Babu abinda yake Haka ni Kuma ban fasa kukan da nakeyi ba. Tun baya kulani har na fara jin tsakin shi lokaci zuwa lokaci. Na saka fuskata cikin palms Dina Ina kuka Wanda yake fitowa daga karkashin zuciyata. " Keeeeeee! Dallah rufewa mutane Baki da wata muryar ki kamar ta gyare!" Babu Wanda ya taba jin muryata Bai so ya kara jinta ba, a hankali nake magana cikin tattausan lafazi, Haka idan kuka nake bawai bude duka muryar nake Ina kukan ba. Wani katon Abu da nake ta kokarin ganin ya wuce a makoshi na ya Kara zuwa ya tokare min, hawayen da kukan memakon su ragu se Kara gudu sukeyi Haka muryata memakon na rage sautin kukan se na Kara fadawa, nasan Babu mijin da zai daki matar sa Koda shi din... Ban ma Gama tunanin ba naji saukar Mari a fuskata, nakai second talatin bana ji, bana gani, sewani dum a kunnena sannan idanuna sun rufe ruf Dan kansu. Nasan Kawu yasha Marina Amma wannan Marin da ban yake. A hankali coordination Dina ya dawo, senaji Abu Yana bin hancina Ina Kai hannu naga jini ne, kunsan duk azabar da nake ciki kasa Koda uhum nayi? Nasa hijab Dina na goge hancin Wanda yasa naji wani sabbabbin hawaye sun Kare balle min, Amma ko sauri Babu. Tafiya mukai sosae sannan muka Isa Kazaure wadda ake Mata take da Kazaure ta Dambu kowa Sarki! Ni dai kaina na a sama saboda na samu jinin ya daina zuba, ban masan iya inda muka ketare ba se ganina nayi yayi parking gaban wani gida, ya kashe motar sannan ya kalleni tareda sakar min harara wadda tasa kayan cikina motsawa, na fasa me yasa nake jin tsoron shi har Haka " Ke jaka ce? Se ance Miki ki bude ki fita?" Hannuna na rawa na Kama handle din kofar na fita, Yana tsaye na mayar na rufe sannan na rufa Masa baya har ya bude kofar ya Shiga, kafata ta dama na saka na Shiga, Ina karanta adduar da Mummy da Ummiey Suka dinga nanata min, hawaye ya cigaba da sakko min, wani na korar wani. Babu abinda kake ji se sniffing Dina, ya juyo ya maka min harara wadda tasa nayi saurin hadiye kukan, gidan safe content ne, parlor muka fara shiga madaidaici, yayi balain kyau tabbas interior decorator ba karamin wonderful job tayi ba. Parlon purple ne light da dark Amma light yafi yawa hakan ya haskaka shi, na shagala Ina kallon parlon, ya shige ciki ni Kuma na rakube gefe guda, se wajen bayan thirty minutes sannan ya fito ba tareda ya dubeni ba ya fice abin shi Yana zura makulli cikin aljihu, na Jima a zaune Ina tunanin abinda bansani ba, naji Kiran sallar laasar, na Mike na nufi inda ke gefe Ina hango kofofi daya na kallon daya, dama Wanda ya shiga a gefe yake, Kuma ya kulle nasan nashi ne. Tunda dama Ummiey tace da Suka zo jere se maida kayan dakin shi akai tunda na 3 bedrooms aka siya. Na bude dakin farko, komai na coffee ne se labulayen ne brown sunyi kyau, Kuma daga gani furniture din sune manya Dan gadon ma abin kallo ne. Na bude dayan shi Kuma Ash da red ne, very simple yet elegant. Na shiga nayi wanka sannan na fito da alwala a jikina , na bude wardrobe Ina kallon yadda aka gyara min kaya, hawaye a hankali ya siraro min, kamar mafarki nake ganin komai, Wai nice me aure, wannan gidan Wai nawa ne nice matar gidan, I couldn't believe it. Nayi sallah na shirya cikin dakakkiyar shadda mustard yellow da Lacy edge Baki, na gyara fuskata kamar yadda aka min nasiha, na daura dankwalin da ba Gama iya daurawa nayi ba, na koma dayan dakin inata bude bude, Amma bawai kallon content din abun nake ba gaba daya hankali na baya Kan abinda nake, nayi nisa sosae Ina ayyana anan Kuma wacce irin rayuwa zanyi? Banga alamar akwai jin Dadi ba, na shafa fuskata da ta Dan tashi saboda Marin da ya zabga min, na girgiza Kai se na samu kaina da adduar Allah ya kawo min dauki! Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam first Bank of Nigeria. Send evidence of payment to 09063467258[05/01, 14:34] +227 98 36 59 34: 32 Hajja Huwaila na zaune cikin daki, tayi rama sannan shekaru sun Kara Hawa kanta duk ta tsufa, balle a yaddaa take jin zuciyata me dauke da mikin kusan shekaru Sha biyu, tun ranar da Malam ya furta korar da yaiwa Junaidu,Kuma Junaidun ya fita Bai Kuma Kara waiwayar gidan ba, Babu wnai dare da idan yazo zata kwanta Bata Yi kukan rashin shi ba, sannan kullum se tayi Masa adduar shiriya sede kullum tana zuba idon kallon kofar gida taga ko zai shigo Amma har yanzun Babu amo Babu labari, har ta gaji ta hakura sede dukda hakan kullum se tayi maganar shi, Amma Kuma wani barin na zuciyar ta na tuhumar ta da rashin tarbiyantar da shi akan daidai shiyasa ma har ya Zama lalatacce Haka. Sadiya ta shigo dakin bakinta dauke da sallama , Amma Hajja din Bata amsa ba, ta zauna cikeda rashin kuzari da Kuma sanyin jikin ganin mahaifiyar tasu a Haka tace " Hajja! Wai se yaushe Zaki sararawa zuciyar ki ne? Shekara Sha biyu fa, kilan ma ya manta dake" Hajja ta saki hannunta tana kallon Sadiya tayi murmushi me ciwo tace " Da zai iya manta uwar shi Amma Ina me tabbatar Miki ko da ya manta Dani ni din bazan manta dashi ba, ba Kuma Zan daina Masa addua ba. Baki San dadin da ba" Tayi kwafa cikeda bacin ran maganganun Hajja tace " Dukkan mu mu biyar Muna nan, muna Miki biyayya Amma kin kwallafa Rai akan wancan gantalallen" " Sadiya! Tashi ki fita min a daki" Ta mike tana zumbura Baki ta fice, ita kam Babu Wanda ta tsana irin Junaidu a ganinta shi ne sanadin halin da mahaifiyar su ke ciki, gashi ita tana yarinya komai ya faru Amma dukda Haka anzo bikin ta seda aka samu matsalar da aka fasa auren ta har sau biyu. Dakin amaryar baban su ta tafi dama nan tafi zama. Hajja ta girgiza Kai tana adduar Allah ya kawo karshen matsalolin ta yasa yaranta su kaunaci junan su. A hanakali taji muryar Fatima dake aiki a tsakar gida tana yiwa Malam sannu da zuwa, ya Kara tsufa kana kallon shi kasan Yana cikin afuwar rayuwa, ko gidan ka kalla zaka San arziki ya zarce na da, ya amsa Mata Yana tambayar ta Hasiya, tace tana daki yace ta shiga tace Mata ta sameshi dakin Hajja yanzunnan. Daga Haka yayi dakin Hajja wadda har lokacin tana zaune Kan sallayar da ta idar da sallar laasar ko motsawa batayi ba. Malam ya shigo bakin shi dauke da sallama, ta dago tana duban shi Bayan ta amsa, Yana Zama Hasiya na shigowa, ta zauna ta gaishe shi tace " Malam lafiya dai ko?' Ya Dan watsar da hannayen shi Yana duban Hajja yace " Hajja maganar akan Junaidu ce" Da mamaki Hajja ta dube shi, wani sanyi Yana lullube zuciyar ta ita dai tunda ya Kori Junaidu Bata tunanin ta Kuma jin ya ambaci sunan shi ko sau daya, Bai Kara maganar shi ba, kamar yadda ya fada ya shafe shi cikin yaran shi to tabbas hakan yake nufi Dan ko da Wasa Bai Kara zancen shi ba, itama Kuma Bata Kara Masa zancen shi ba, Hasiya ce ma takan kawo maganar shi Amma idan ta Masa se yayi Mata shiru Amma dukda Haka Bata fasa ba, Dan a ganinta tsakanin ta da Hajja Huwaila akwai babbar amana, abinda ya shafe ta ya shafe ta itama Dan hakan Dole ta Taya ta jimamin abinda ya sameta. " Eh shidai Junaidu, maganar shi ce ta kawo ni. Dazun aka daura Masa aure..." " Aure? Waye ya bashi 'Ya?" Hajja tayi saurin tambaya, Dan last time da zainab din Fatima tazo yace Mata ta ganshi yayi kudi dake kusan unguwa daya suke zaune Amma tace Mata kowa a unguwa Yana fadar halin dai da suka San shi dashi tun Yana gida. " Tohm bansan yadda Zan Miki bayani ba, Amma dai yayi aure, yarinyar marainiyar ce kawunta ya aura ma Junaidu Wanda sauran kawunnan nata sun kasa fahimtar dalilin shi na yin hakan ba, ko ni da nake mahaifin Junaidu ace Allah ya hallata na aurawa Sadiya ko Ambaby shi tabbas da bazan bashi ita ba. Na tabbatar duk inda yarinyar take tana cikin damuwa, Dan hakan nake so kuje ke da yaran ku ganta kafin Kuma tazo nan" Hajja hawaye suka Shiga sakko Mata Wanda ta rasa na menene, ita dai ba farin ciki take ba hakan Kuma ba bakin ciki take ba sema hope da take ganin zai Zama silar shiriyar danta, a ganinta ni din Zan Zama wani tsani na gyara Mata danta. Hasiya ta mike itama cikin farin ciki tana duban Hajja tace " Ban ma taba kawowa zai kalli mace yace zaiyi aure ba, da izinin Allah adduar ki ce ta karbi, Bari naje na gano sabuwar Yar tamu" Ta fita ba tareda ta jira amsar Hajja ba, tana fitowa tsakar gida ta shiga kwalawa sadiya da Ambaby Kira Wanda su kadai Suka rage a yayan su Mata basuyi aure ba, tunda dama ba wani yawan gaske ne da yaran ba. Suka fito Suka same ta a daki tace musu su shirya zasu unguwa, kowacce da murna Dan ba fita suke sosae ba Suka tafi shiryawa. Tana yafa mayafi taji sallamar Jidda matar Jazuli yayan Junaidu, ta shigo kamar yadda ta Saba se ta fara shigowa gurin ta kafin taje wajen Hajja ma, wannan Hajja ta koya musu girmama Hasiya. Hajja sukaiwa sallama sannan Suka fita, Jidda nata tambayar inda zasu je, Malam ya Basu kwatancen gidan Suka tafi. Bayan na Gama binciken da banma San me na gani ba, na dawo parlor na zauna na tafka uban tagumi Ina tunanin yadda rayuwa take zuwa ma mutane, ni dai tawa bansan yaushe Zan bude shafin da zanyi dariya ba, bansani ba ko bazan Yi dariyar ba ko Kuma se nan gaba. Kwankwasa gidan yasa na Mike Ina mamakin waye, katon clock din dake manne jikin bango na kalla karfe biyar da mintina, daki na wuce na dakko bakin veil din dana riga na fito dashi, na yafa sannan na fita zuwa bakin kofar nace " Wannene?" Dukda jira nake naji muryar me gidan yace ubanki ne, Dan nasan wannan karamin aikin da zai iya ne. Muryar babbar mace naji tace " Kannen Junaidu ne" Who's Junaidu? Na tambayi kaina, se lokacin kaina ya tuna sunan me gidan kenan, cikin hanzari na bude kofar tareda Dan ja da baya Dan na Basu guri su shigo, wadda ta fara shigowa Gwoggo ce wato Hasiya, se Kuma Yan Mata biyu sannan Anty Jidda. Na saki fuskata dukda murmushin da nake Bai Kai zuci ba Amma dai naji dadi da wasu Suka nuna sun damu Dani. Jidda ta kulle gidan na musu sannu da zuwa sunata Bina da kallo har muka shiga parlon, Ina jin yadda suke gasping na tsananin kyan da parlon yayi, na musu tayi su zauna sannan na zauna saman carpet " Ina wuni?" "Lafiya Lau" Ta amsa ni Ina iya ganin tsanin farin cikin da take ciki, sauran Suka gaishe ni na amsa Ina Wasa da hannuna " Ina Junaidun?" Nayi Dan Jim kafin Kuma nace " Mhm ya fita" Ta gyada kai, Anty jidda tace min " Ya sunan ki?" Ina Dan murmushi nace " Amina sunana" Ta gyada Kai sannan na Mike Ina tunanin yadda Zan samo musu abinda zasu Sha, na nufi kofar da nake tunanin kitchen ne, na tura nan na samu carton din ruwa lode, wata ajiyar zuciya na sauke ba tareda na bi takan kallon kitchen din ba na dakko glass tumblers na kawo musu, sunata min sannu. Na dubi ta gefe na nace " Ya sunanki?" Tace " Sadiya, wannan Ambaby mu kannen shi ne, wannan Anty jidda ce ita matar yayan mu ce, ya girmi mijinki. Wannan Kuma Gwoggo ce " Na gyada kaina na fahimta nace " Nagode!" Daga Haka mukai shiru se can Suka Mike zasu tafi, na Mike na rasa me Zan Basu, se na tuna ai Naga containers din gara a kitchen, cikin sauri naje na babbude na diba musu me yawa na kawo musu tareda musu rakiya har bakin kofa, nace da " Dan Allah ki dinga zuwa. Gwoggo nagode sosae" Na fada Ina jin tun bayan rasuwar Abbuna ga Wanda suka nuna min kukawar su. Ciki na koma Ina ayyana nayi Saar in-laws ina fatan Zan iya Zama dashi, Ina fatan halayen shi zai gyaru. Ruwan da Suka Bari na tattara na Kai kitchen na shiga bandaki nayi alwala jin har an fara Kiran maghrib, nayi sallah sannan na zauna Ina tunanin inda Zan samu fitila na haska, Dan duhu ya fara Shiga, Allah ya kalla sincere zuciayata se gashi an kawo NEPA, nayi sauri na Mike Ina hamdala, wata Leda na hango a kasa, alamar Ina janyo Kaya ta fado, nayi sauri na Mike na dakko ledar a take naji farin ciki ya mamaye ni ganin waya sabuwa a ciki, na dakko na saka caji sannan na zauna gefe Ina jin yadda cikina ke kugin Yunwa, har wani ciwo ciwo yakeake min. Wasa Wasa har ishai banji shigowae shi ba, hankalina ya fara tashi ga Kuma Yunwa ga tsoron ni kadai ce a gidan. A lokacin wayar ta cika hannuna na rawa na kunna ta, hatta Sim da komai is set, na Shiga contact Dina number mummy na gani da sauri nayi dialing Babu jimawa ta katse Sega kiranta ya shigo, hannuna karkarwa yake na Kara kunnena nace " Mummy!" " Daughter? Ya kike? I'm very sorry I failed you again" Na danyi murmushi me ciwo na gaishe ta tana ta bani hakuri tace min " Ban San yadda zamuyi ba Afiyya Amma ban taba ganin tashin hankalin irin na yau ba, kiyi hakuri kiyi addua itace mukai sake bamuyi ba, itace sakacin da mukai har Sa'idu ya samu ya dinga controlling dinmu, Ina son kiyi addua ni Kuma I'll do whatever it's in my power Naga na raba aurennan!" Motsin da naji yasa nayi saurin Mata sallama, nayi silencing wayar na fito, yana tsaye a parlon Yana kallon kofar dakin Dana fito daga ciki, na karaso Adan dadare nace " Sannu da zuwa" " Kawo min ruwa" Na juya na dakko Masa ruwa da tumbler na dawo na sameshi ya zauna cikin daya daga cikin cushions din da Suka kawata parlon, na aje Masa tareda Zama can nesa dashi Ina rarraba idanu ganin ko ya shigo da abinci, can nace " Dazun Gwoggo tazo da...." " Wacece Gwoggo? Uban waye yace ki bude min gida mutane su shigo min?" Gabana nata faduwa nace " Kannanka ne" " Nace Miki inada dangi ne? Wallahi wannan shi ne na karshe da Zaki budewa wasu gidannan. Tashi ki bani guri" Na mike Babu musu na kwashe kayan gaban shi na Kai kitchen sannan na dawo, Yana nan zaune nayi ta maza nace " Banci abinci ba!" Ko kallona baiyi ba balle na saka ran ko yaji abinda na fada, nayi Dan Jim sannan na nufi daki Amma se naji idan nayi bacci da wannan yunwar to kilan mutuwa zanyi. Na mike na cire kayana nasa kayan bacci na zumbula hijab na fita parlon. Yana nan inda na barshi, na Kara matsawa nace " Banci abinci ba!" " To ki cinye ni Mana idan ke mayya ce! Kin ishe ni fa" Nayi saurin ja da baya saboda yadda hargagin shi ya tsoratar dani, nayi saurin juyawa Zan tafi daki se na tuna kayan gara na bude kitchen na dauki diblan da alkaki naci sannan na koma daki na zauna naci nayi brushing sannan na kwanta, banma kawo zai zo dakina ba Dan hakan na saki jiki nayi bacci! Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment to 09063467258. [05/01, 14:34] +227 98 36 59 34: 33 Juyi kawai nake saman gadon dan Babu wani bacci ma da yayi kokarin zuwa ya dauke ni, na Jima a Haka da wayata a hannu Ina ta bubbude social media accounts, na bude WhatsApp da Wattpad, se Sabin Gmail account. Inata tunanin yadda Zan yiwa kaina Shirin zaman wannan gidan, da dukkan alamu Babu wani zaman lafiya ko farin ciki a cikin tarayyar mu. Ga daga farawa har an fara da horon Yunwa kenan an gudu ne baa tsira ba. To idan hakane se nace gwara zaman gidan Kawu Sa'idu akan wannan. Can wajen biyu Naga to da wannan tunanin da nake zaifi ace Allah na kaiwa karar dukkan abinda yake faruwa. Na mike nayi alwala na dawo na kalli gabas na fara sallah, dake shedan babban makiyi ne se na fara Hamma Ina jin bacci, Haka na Dan kwanta Ina tasbihi bacci ya daukeni, bani na farka ba seda ana iqama, cikin hanzari na sake alwala sannan nayi sallah na Kara bingirewa nayi bacci a gurin. Wajen bakwai ringing din wayata ya tashe ni, na bude idanuna a hankali se Naga garin yayi haske hakan yasa na Mike da hanzari na dauki wayar, bakuwar number ce tunda dama banyi registering contact din mutane ba, seda na fara wanka sannan na shirya cikin wata atamfa skirt da riga ban daura dankwalin ba se na saka hijab na fito parlon, Babu alamar an fita Haka Babu alamar ya tashi, kitchen na shiga na wanke tumblers din da nayi amfani dasu jiya kafin na fara tunanin me zanci, Yunwa nake ji kamar zanci Babu. Tukunya na dakko na daura ruwan zafi na fito na tsaya nayi shiru ina tunanin ko dai na tashe shi nace Masa Ina jin Yunwa, se na tuna yadda mukai dashi jiya, yace min idan ni mayya ce to se na cinye shi, idanuna suka ciko da kwalla na tausayin kaina, Amma se Naga me yasa Zan fara kuka tun yanzun? Idan har na fara to tabbas zuwa nan da wani lokaci lacrimal gland Dina zai daina secreting tears. Kitchen na koma nayi shiru Ina kallon yadda komai ya tsaru a ciki, komai ka kalla kasan an narka kudi, na goge hawayena, dama da wannan abin da kudin da suka kashe Wanda nasan daga aljihun su yake inama tsayawa sukai akaina, Suka zaba min rayuwar da zanyi farin ciki, Dan Ina da tabbacin duk abinda aka siya min ba daga gadona bane nasan daga aljihun su ne, mistake daya sukai na barina hannun Kawu Sa'idu Wanda shi ne dalilin lalacewar komai a rayuwata! Kan fridge na hango wani tray an jera gwangwanin Madara da sauran kayan tea, yadda kuka San anyimin albishir da Shiga aljanna Haka naji, na dakko na aje Kan kitchen island din sannan na zuba tea bag a ciki ya Kara tafasowa, Ina tsaye Banda murmushi Babu abinda nake, tunda aka fara bikinnan Babu abinda yayi min farin ciki irin ganin kayan tea dinnan, na hada shayi me kaurin gaske Wanda rabo na da Nasha me kaurin shi tun Ina gidan mu. Na zauna na dakko cake cikin kayan gara naci sannan na zuba Masa a flask na fito dashi parlor na aje. Kitchen na koma nayi gyare gyaren abubuwa har lokacin Bai fito ba, na dauka cake na saka cikin transparent dish na kai Masa. Ina bincike a kitchen din Naga stew cikin bucket ai tuni na Nemo tukunya na juye ta nayi warming sannan na Nemo container na juye na bar wadda zanyi amfani da ita a tukunya na zura cikin fridge. Motsi naji a parlor hakan yasa nayi saurin fitowa, shi dinne ya fito cikin coffee jallabiyya, fuskar shi a murtuke Yana kokarin hada TV, na karaso na zauna can nesa dashi nace " Ina kwana?" Bai amsa ba Haka Bai juyo ya kalleni ba, har seda ya gama sannan ya zauna na kalle shi nace " Na hada maka tea" Ya gyada kai, na karaso na hada Masa tea sannan na bude mishi cake din, ya kalleni cikin Isa yace " Meye wannan?" Na Dan hadiyi yawu nace " Cake ne!" " Ba zanci ba!" Ya fada Yana ture dish din Wanda Banda na rike Babu abinda zai hana shi fashewa, why is he so aggressive? Na tambayi kaina, dauka nayi na koma kitchen ban Kara bi ta kanshi ba, daki naje na zauna na tarar da calls din da nayi missing, Mummy na fara Kira muka gaisa ta fada min inda kayan gara ta suke wato foodstuffs, ta Kara koya min dabarun Zama da Kuma hakuri. Ina gamawa Uncle Babawo ya kira mun Jima muna waya sannan Rooks dasu Nads Suka Kira, Nads nata tambayar yadda first night Dina ya kasance, takaici yasa na kashe wayar, se daga baya Rooks ta kirani " How's it over there? Ina fatan Babu matsala" Na danyi murmushi marar sauti nace " I'm fine! Zaki zo ?" " Mummy tace zamu zo kafin mu koma, akwai abinda kike so ne?" Na gyada Kai na kamar tana gabana nace " I need contraceptive pills please" Da mamaki tace " Planning zakiyi? Akwai abinda ya Shiga tsakanin ku ne?" Na girgiza Kai nace " A'a Babu Amma I want an armor, yadda Zan Kare kaina" Cikin rashin fahimta tace. " But why Afeey?" Nace "Ba Zaki gane ba Rooks life is not what it's seems! Duk yadda zanyi Miki bayani ba Zaki gane ba, Amma ni dai bazan iya hada zuria dashi ba" " Ke!!!" Naji maganar shi Yana tahowa towards dakina, na Yi saurin Yi Mata sallama akan zamuyi magana na aje wayar na fito , wani irin kallo yake min na rashin mutunci irin ni banza dinnan ce, nace " Gani!" " Ke bakiji Ina kiranki ba? Ke dabbar Ina ce" Na dauke kaina gefe cikin kasa da murya nace " Ni ba dabba bace" OMG! Ashe ya jini kawai se ji nayi taf ya wanka min Mari, " Keeee! Baki San ni waye bane ko? Waye dabban idan bake ba Dan uwarki?" Na mishi banza na dauke kaina, fuskata ya juyo dashi Ina fuskantar shi yace " Waye dabban?" Na fara kici kicin kwace fuskata, ya da hannun shi tun karfin shi ya hankade ni na tafi ta baya na buge kaina da abin shoe rack dina, na rike kaina naki dagowa saboda yadda nake jin azaba a cikin kaina, yaja tsaki sannan ya juya ya bar wajen, na Jima a gurin Ina kuka sannan na koma daki na wanke fuskata, na kwanta nayi shiru Ina jin daci a cikin Raina har cikin bakina. Wajen azahar na daura shinkafa nasa cikin flask sannan na zuba nawa Amma da na dauki spoon se na kasa ci, na rufe fuskata na saki kuka, meye makoma ta a cikin wannan auren? Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment to 09063467258 [05/01, 14:34] +227 98 36 59 34: 34 ⭕Matured content! Ina ta juya abincin Wanda yayi sanyi sosae, da na tabbatar ba zanci abincin ba se kawai na rufe na fito parlon, dama tun kafin azahar ya fita, jin ana kwankwasa kofa yasa na wanke fuskata da sauri Baki na dauke da adduar Allah yasa su Ambaby ne. Fitowa nayi sanye da hijabi, banma tambayi waye ba saboda na sawa zuciyata kawai ita din ce na bude kofar, na samu wasu Yan kananan Yara ne Basu fi shekaru goma zuwa Sha biyu ba, na matsa musu suka shigo sannan na maida kofar nayi jamming, tare muka Shiga parlor Suka zauna na tambaye su daga inda suke a amsar su na fahimci daga yaran neighbors Dina ne. Na zuba musu abinci sannan na koma kujera na zauna deep in thoughts. Bayan laasar na fito daga daki na idar da salla nazo na cewa yaran bazasu tafi gida ba saboda kada a neme su, Naga mutum a tsaye, jikina har rawa yaso farawa saboda tsorata da nayi, nayi kokarin danne tsoron da nake ji saboda nasan zai iya using wannan tsoron da nake mishi ya gallazawa rayuwata, tunda kwana biyu kawai nayi Amma Ina jin tamkar I'm living in a hell! Yana tsaye ya zura hannayen shi a aljihu Yana kallon yaran da I'm not sure idan sun San da shigowar shi ma, na karaso jikina a sanyaye Dan banso ya samu yaran cikin gidan ba saboda warning din da yayi min akan barin mutane su shigo. " Su waye wadannan?" Na kalle su sannan na kalleshi na rasa me zance Masa saboda tsoron magana nake ma ya kaimin Mari, fuskata has had enough slaps. Ya daka wa yaran tsawa duka Suka fice har da me manta dankwali, jikina se ya fara rawa Dan nasan ni ce next, kafin ya ankare nayi saurin juyawa na nufi daki Amma Ina shiga Ina kokarin rufe koafr na ganshi a bayana, na ja da baya idanuna a warwaje kana kallon yadda kirjina ke kasa da sama, ya tura dakin ya rufe sannan ya matso inda nake tsaye Ina tunanin yadda zan Kare kaina, yayi shiru yana kallon fuskata wadda da ace shi me Imani me kamata yayi ya rungume ni ya shafa bayana ya rada min a kunne cewar everything will be ok? Ashe shi tunani yake lokaci yyai da boka ya fada Masa, idan ya kusanceni to tabbas burikan shi zasu cika. Ajiyar zuciya ya sauke tareda saka hannun shi ya angaza ni na fada Kan gadon, kaina ya bugu da katakon gadon wani azababben zafi ya ratsa kwalkwalwata da dukkan jikina, Babu shiri na saki wani ihu Wanda yasa yayi saurin sakina alamar ya tsorata, ganin ba wani Abu bane yasa Bayan hannun shi ya buga min a fuska a take hancina ya fara jini, saboda dukan ya kai. Na saki kuka marar sauti bani ma da karfin yin me sauti, ya dage skirt din jikina ba tareda wani romance ko wani Abu ba ya fizge pant din jikina, it's more like a rape than normal marital affair! Wani ihu na saki Ina kankame jikina, tamkar Zan hadiyi zuciyata Haka naji lokacin da naji bare skin din shi na gugar nawa bare skin din, ture shi nake Amma Ina Bai ma ji, se wajen minti uku naji banji komai ba se tsaki da ya saki tareda ture ni gefe, nayi saurin tashi nayi toilet na kulle na daura kaina kan sink na saki marayan kuka, kuka nake da karfi zuciyata da dukkan jikina kunci suke, kuka nake na rashin madafa, na rashin gata, na rashin sanin yadda zanyi, Ina jin kaddarar tayi min tsauri, a Haka Zan cigaba da rayuwa, I'm been molested, wacce irin rayuwa ce wannan? Nayi kuka har bansan iyakar lokacin da na dauka a toilet din ba, se a karshe na fito na samu baya nan. Tun daga nan na rufe kaina a daki na fara laluben cikin drawer inda nan Rooks tace min ta aje min sako. Wani Dan karamin diary na dakko daga ciki, na kalla diary take na tuna shi, why did I forgot about it? Na tambaya kaina da mamaki, na kalla buttons din na tuna a cikin jirgi yake cemin passcode din date of birth Dina ne, na kankame littafin na saki kuka Ina fadin " Abbu I missed you, Abbu ka barni cikin wahala" Na dinga kuka Ina jin wata irin kewar shi tana Kara mamaye Raina, iyaye sune komai lokacin da suna da Rai Babu abinda na rasa, kowa Sona yake, kowa kaunata yake, duk inda naje rubibi na ake Amma kalleni yanzun, ni dinnan dukka gata na cikin kiftawar idanu komai ya lalace, banida wani gata, banida wanda Zan saka kaina akan kafadar shi nayi kuka, wannan itace rayuwar? I'm been tortured a hakan yanzun Zan cigaba da rayuwa? Na Kara sakin kuka na bare bakina wanting to pour out my heart all, Ina son naji zuciyata tayi wasai, bana son naji Koda digon bacon Rai, nasan na rike da yawa at this rate Ina jin kamar zuciyata zata fashe kamar bakin ciki zai kasheni. Na Gama kuka na sannan na Danna code din se gashi ya bude, na fara shafa littafin rubutun shi ne a ciki, ta gefe pictures Dina ne, title din chapter ARRIVAL OF OUR PRINCESS! kalamai ne masu Dadi masu sanyaya zuciya Wanda zasu tabbatar maka ko daga wanne baki ya fito to tabbas ba karamin son Wanda aka rubuta danshi suke ba. Na saki kuka Ina fadin " Abbuna!" Ganin kamar zanyi hauka yasa na rufe na Yi alwala nazo na dauka casbaha na fara ja, a hanakli naji nutsuwa tana saukar min, se naji kamar an bude zuciyata damuwa ta na evaporating cikin iska! Junaidu ya kalla kanshi, ya kalli kofar Dana kulle yana iya juyo ihun kukan da nake, ya Kara kallon manhood din shi dake a kwance Babu alamar erectile muscles dinsa na aiki, ya Mike a mugun fusace ya maida wandon da sannan ya fito daga dakin, hannun shi na rawa ya fara Kiran Safiyyu " Yane angon Amina?" Ya buga tsaki yace " Taki tashi!" Cikin rashin fahimta Safiyyu yayi dariya yace " Ka haike ma yar mutane Allah yasa baka kashe ta ba, wa yaga farin Shiga, ko nazo muje asibiti?" Ran Junaidu ya Kara baci yace " Banma shiga jikinta ba, abar Taki tashi kwata kwata..." " What?!" Safiyyu yayi exclaiming cikin mamaki yace " Me ya faru?" " Da na sani Zan kiraka ne? Fada min zakai yadda zanyi, golden time din na tafiya fa!" Safiyyu ya fara tambayar shi yadda akai ya fada Masa shi kaiwa afka min yayi, Safiyyu ya dinga dariya yace " Malam ai ba Haka zakai ba, se kayi romancing dinta kafin..." " Kaga ni fa Banda wannan Saar bana tunanin Zan taba kallon mace naji wani shaawa" " To Haka zaka Bari lokacin ya wuce, nasan ba sonta kake ba ba zakai shaawarta ba, to Amma idan ba Kai amfani da ita ba kenan kawai Sa'idu ka cikawa burin shi, kaga ya samu dukiya sannan ya saka kana bawa yarinyar da Bata ji bata gani ba wahala, kaci sadakin ka !" Haka yayi ta zuga shi har ya amince, nikam nayi wanka na fito saboda yunwar da nake ji, Babu abinci alamar ya shigo yaci kenan, spaghetti na dakko na dafa daidai cikina Dan bazan bashi abinci ba, alkawari nayi tunda zai iya daga hannu ya dakeni to tabbas na daina dafa mishi abinci. Ina Gama sauke taliyar na juye cikin collander, nasa stew din cikin microwave na fara warming, tana gamawa na juye a plate har lokacin bawai Ina jin ni din farin ciki nake ba Amma dai Babu laifi na samu sauki. Na fito rike da plate dayan hannuna da ruwa, shi baya sallama Dan Haka ban maki shigowar shi ba, Yana zuwa tamkar wani dabba ko Dan dabba ne tunda dabbbobi kawai ke amfani da wannan approach din ga partners dinsu. A tsorace na saki plate din hannuna ya tarwatse Haka ruwan ya bi nashi gurin, ya janye hijabina Wanda ya bayyana rigar dake jikina, Bayan nayi wanka Naga Babu amfanin saka Kaya kawai se na dakko daya daga cikin kayan baccina thigh lenght silky milk, duk kirjin net ne me Asalin kyan gaske, tayi exposing dukkan boobs Dina a waje, ya keta rigar wadda ta bayyana jikina take na silale kasa a kokarin Kare kaina ya bini ya fara exploring jikina, ana cewa wannan abin nada Dadi ko? That's idan zuciyar ka da gangar jikin ka ta amince, ni din Banda ciwo kunci, bakin ciki, tsoro , bacin Rai Babu komai a cikin zuciyata, Ina kallo ya raba kanshi da kayan jikin shi, ya daura bakin shi a nawa duk yadda nake kokarin kaucewa ban iya tserewa wannan awful kiss din ba, it was a moment da bana son a rayuwata na Kara tunawa, it was the most hardest moment of my life, Ina ihu Ina komai Ina Kiran sunan Allah, Ina kwalawa Rooks kira, Ina neman taimako se naji an hankada ni for the second time his manhood refuse to erect, ya saki wani ihu tareda yin wurgi da wani flower vase dake Kan center table, yana zuwa bango ya baje Karin aiki kenan, nayi saurin mikewa na nufi dakina Ina adduar Ina ma na koma gidan Kawu Sa'idu ya fiye min wannan zaman balain da kuncin! Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment through 09063467258.36 Mu muna daki bamu San abinda take faruwa a parlor ba, Rooks nata kokarin ganin ta fahimtar Dani akan na dauki zaman mu dashi a matsayin jihadi, nayi kokarin daidaita rayuwar shi, kilan shi ne dalilin da yasa Allah ya kaddara auren mu, nidai nasan a kur'ani ance mace ta gari ta miji nagari ce, Dan Haka na sawa Raina ko ba yanzun ba ko da watarana ne se na rabu dashi, Kuma jikina na bani komai ya kusa zuwa karshe. Se yamma sannan Suka dauki hanyar tafiya, banyi kuka tunda Banga amfanin kukan ba, I've cried enough da ace kuka na canja ma mutum rayuwa tabbas da tuni bana cikin kuncin da nake ciki. Har gate na raka su Ina kallo suka tafi, na maida kofar na rufe na dawo na zauna a parlor very deep in thought, to Babu abinda zanyi seda suka gyara min komai da komai sannan Suka tafi. Ina nan zaune har dare yayi se wajen Sha daya naji motsin shi, ya shigo yadda Bai cemin ci kanki ba Haka Nima bance Masa ba, na maida hankalina akan kallon da nakeyi. Dakin shi ya wuce na zata bacci zaiyi Dan Haka na Kara sakin jikina deeply immersed a tunani, Dan ba ma gane abinda akeyi nake ba, tunani na duka Yana kan maganar da mukai da Rooks, nasan duk maganar da ta fada gaskiya ce Zan iya Zama silar shiryuwar sa but that's only idan Yana sona, to nikam kullum kallon da yake min kallon tsana ne da irin Bai taba ganin Abu so disgusting like me ba. Na sauke ajiyar zuciya Ina jin ta Ina Zan fara? Ya kamata na saka shi ya fara sallah but ta Yaya? Banma San Wasa nake da bakin wuta ba se washegari, very early na tashi wannan macaroni da banci ba saboda zuwan su Rooks na dafa na zuba cikin karamar warmer na aje sannan na danyi gyare gayren da ba zaa rasa ba na Yi wanka na shirya cikin bakar Abaya gashi na na kalla gaba daya ya cunkushe Ina bukatar kitso, duk lalacewar zamana a gidan Kawu Sa'idu Ina zuwa kitso. Na dakko comb na taje na saka band na kulle Kan na daura dankwalin abayar, Dana fito ya riga da ya fito Yana zaune kana kallon shi kasan Bai wanke fuska ba, na karasa nace " Ina kwana?" Bai cemin komai ba Wanda yasa na fara jin haushin dalilin da yasa na Masa magana ma in the first place. Kitchen na wuce na zauna na zuba Mai da yaji naci abincin da duk yadda na Kai da rashin cin abinci da yawa Bai gamshe ni ba. Na Sha ruwa na fito Yana nan inda na barshi se kawai na shige daki na kwanta Ina juyi Ina jin matsananciyar Yunwa na addaba ta. Kwalla min Kira yayi yasa na fito, alamar zai fita Dan yayi wanka ya Kuma canja Kaya, ya dubeni da ga sama har kasa yace " Ki shirya zakije can gidan' Na gyada kaina ba tareda nasan wanne gidan yake nufi ba, ciki na koma na canja kayana zuwa zani da riga na atamfa na dauka babban veil na yafa sannan na Dan tsinci abinda zanyi tsaraba dashi na fito, yayi gaba na bishi a baya, a kusan watanni biyu wannan ne Karo na farko Dana saka kafa ta a wajen gate, banma San ya yanayin unguwar yake ba, duk yadda ya kamata na Shiga makota na Amma ko kadan ban shiga ba, wa ya Isa ya barni inama Naga fuskar tambayar. Motar shi na Parke kofar gida se kyalli take, wani yaro a tsaye ya samu kwankwalatin lemu ya fara karto Masa mota tun daga farkon bomber zuwa karshe, kwankwalatin Nan ya cika Tam da paint din shi, nayi saurin saka hannuna na rufe bakina tausayin yaron da iyayen shi suka Kama ni, nasan yau rashin arzikin da Junaidu zaiyi se inda karfin shi ya Kare, ga yaron ya kusan 10years hakan ya nuna Yana sane yasan abinda yake ba daidai bane. Na kalle shi na dubi yaron da ya Yar da kwankwalatin ya nufi gidan su a guje, Junaidu ya cire rigar shi ta bayyana farar singlet din dake jikin shi, ya wullo min rigar a fuskata ya take kafafun shi yabi yaron nan da already ya riga ya shiga gidan su, na bishi da sassarfa Dan kada ya Shiga gidan mutane Amma nasan ni wacece, Ina zuwa ya Kama yaron Yana dukan shi tun karfin shi, ga uwarshi nata balai Amma ba zata iya kwatar shi ba. Na karasa na ruke hannunshi ba tareda nasan nayi hakan ba, saboda dukan yadda kuka San saan shi yake yiwa. " Dan Allah ka rabu dashi, Dan Allah!" Na fada Ina rike hannun shi, ganin yadda nasa karfina gaba daya na rikeshi, se yasa hannun shi ya bugeni, nayi baya tamkar Zan Fadi wata budurwa a gidan ta Dan girmeni ta rikeni seda na tsaya da kafafuna kafin ta sakeni, ya saki yaran Yana karbar ko nace yana wartar rigar shi a hannuna ya fice, da sauri nabi bayan shi na samu sunyi kicibis da Wanda nake tunanin shi ne baban yaron, " Wa yace ka.shigar min gidana? Na Dade da sanin Kai jahili ne Amma bansan abin naka har ya Kai Haka ba, Dan Haka yau ofishin Yan sanda zaka kwana" Banyi tunanin zaiyi Masa shiru ba Amma ga mamakina se Naga ya wuce ta gefen shi, hannun shi ya rike tareda fadin " Ina zaka je kake tunani? Ka shigar min gida ka Kuma Dakar min Dana sannan kace zaka tafi, karya kake wallahi!" Junaidu ya dubeshi ya Kuma dubi hannun shi dake rike hannun mutumin, nasan he's going to do something stupid, nayi saurin kallon mutumin nace " Dan Allah ka sake shi, ka bashi hakuri Dan ka ya Karta Masa mota" Ya min wani mugun kallo da inaga ko Junaidu Bai taba min wannan disgusting look din da yasa naji ni totally embarrassed irin kallon da mutumin yayi min ba " Rufe Mana Baki karuwar banza karuwar wofi, mu munyi tunanin babbar mace ce ma Ashe kece" Se nayi shiru Ina jin jikina yayi balain sanyi, karuwa? Na tambaya kaina Ashe ban sani ba kallon da duk Yan unguwar kemin kenan ni din karuwar shi ce, suna ganin Babu iyayen da zasu dauki Yar su su bawa Junaidu aure, take na ja kafafuna da nake jin Kamar anyi musu duka na nufi jikin motar shi Ina tsaye, mutane suka taru saboda police har sunzo, ni ba damuwata abinda suke ba, damuwata kallon da ake min da nuna da ake Yi shi ne matsalata gashi Kuma ya kulle gidan sannan a yadda temper shi take high Ina Masa magana zai iya nada min duka cikin mutanen nan ba damuwar shi bace. Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 0906346725837 Ina daga can gefe idanuna s unyi ja, a karamar shekara ta na kunshi bakin ciki kalakala Amma kowanne idan yazo Ina ganin kamar Zan iya coping se na kasa, baa taba sabo da Shan wahala. Tabbas ance kudi masu gidan Rana, quite sure kowa yasan yaron ne bashi da gaskiya Amma Junaidu ya dauki hukunci a hannun shi, ya Shiga gidan mutane sannan ya daki Dan mutane duka irin Wanda zaka yiwa saan ka, yaran duk fuskar sa tayi kacakaca da jini Amma a haka police officer ya cahrge iyayen shi akan se sun gyara Masa damages sannan su bashi hakuri Kuma, instead shima ayi charging dinsa for assault se suka kyale shi. Ina ta kallon ikon Allah, Haka Suka juya Bayan sunyi musabaha dashi suka tafi su Kuma parent din yaran suka dauki dansu zuwa asibiti, gashi tunda daga gidan kasan karamin karfi ne dasu Amma ai ya kamata ace ya biya kudin ko da magani ne. Muatnen gurin se tsine Masa suke suna fadain daga shi har Wanda ya rabe shi a wuta zasu, ni dai duk a tsorace nake ya dubeni ba tareda ya min magana ba ya bude gidan ya shiga, na bi Bayan shi cikin sauri jin an fara cewa ki jefe su, Ina Shiga dutse Yana bugan gate din, na sauke ajiyar zuciya Ina godewa Allah da Bai sameni ba, na shiga parlon na sameshi yayi daidai da drink a hannun shi Yana sha, ko Zama banyi ba aka Kira azahar naje nayi alwala na dawo na samu ko matsawa baiyi ba, nayi sallah na dawo nace Masa " An Kira sallah gashi har an idar ma!" Yayi min banza kamar yadda ya saba, maimaikon na kyaleshi se nace " Ba kyau abinda kake Yi, abinda yake raba Arne da musulmi sallah ce kawai, tunda Suma a cewar su ai suna azumi Amma sallah ce basayi, Kuma idan kana sallah in har ta karbu ko sauran ayyukan ka baa dubawa..." " Keeeeeee! Ni saan ki ne?" Naga karfin halina nima, nace " Ai waazi ba se saa ne yakeyi ba, baka ganin malamai nayiwa shugaban kasa waazi ba? Hakkina ne na fada maka gaskiya Dan idan ka mutu a Haka Allah kadai yasan me zai ma..." Ban ma karasa ba naji saukar kyakyawan Mari a saman kuncina, na Mike tsaye idanuna Suka ciko da hawaye Amma har lokacin bakina yaki yin shiru na cigaba da fada Masa abinda ya kamata a fada masa aka ki fada masan, ni kaina nayi mamakin daga Ina na samu wannan confidence din? Ban taba ganin bacin ran shi irin wannan ranar ba, ya dakeni kuwa ranar, Dan duk jikina seda yayi birdin dukan da yayi min, nayi ta kuka a daki ni daya Ina jin duniyar gaba daya tayimin zafi but I still have to pick myself up, tunda Allah yasa ba mutuwa zanyi ba to ya kamata nasan abinyi, bazan cigaba da Zama cikin wannan rayuwar ba, Dole na nemawa kaina mafita. Watanni biyu suka Kara Hawa akan Wanda nayi a gidan shi, ya tsiri wasu halaye Kuma na daban kullum se ya dakeni ko nayi Abu ko banyi ba, idan zai fita se ya daina barin gidan a bude se de ya rufe ni ta waje, gaba daya na hargitse banida wani aiki se kuka se plotting yadda zanyi na bar gidan, Babu Wanda ya Kara zuwa gurina se mummy da Rooks shima har kofar gidan suka zo Suka kirani se kawai nace ai bama nan munyi tafiya to ta Ina Zan fada musu cewar ya kulleni ne a gidan, lokuta da dama Ina jin ana knocking Wanda nasan Yan gidan su ne Amma Babu halin shigowa,zancen abinci sau daya ne a Rana yake bani, I remembered na taba jin suna waya da Kawu Sa'idu kafin ya fara bude min wuta sosae " To Kai me kake tunani? Ni kaina bansamu abinda nake so ba, ai cewa akai se na kusance ta kafin burina zai cika, ni banyi ba Banda asara me auren ta ya tsinana min?" Daga dayan bangaren Kawu Sa'idu yace " Ni kaina bansamu abinda nake so ba Sabida Kai dinne madaogara, Amma ya zaayi kace min ka kasa kusantar ta Bayan na aura maka ita" Junaidu ya dunkule hannun shi yace " Zancen banza kenan! Idan Haka ne Zan sake ta Dan na gaji da ajiyar ta tunda ba amfani take dashi ba" " Baka amsa tambaya ta ba, me ya hanaka ka kusance ta, Kuma ya zaka saketa bamu cika burin mu ba" Se lokacin Junaidu ya Masa bayanin Ashe Erectile dysfunction or damun shi, an samu hakan bayan dogon bincike da akai a asibiti suka fahimci trauma ne na dukan da Yan sanda Suka ta Masa lokacin samar takar sa, ranar yini nayi Ina farin ciki a ganina Allah ne ya fara saka min duk zalincin da yayi min. Nafi tunanin a wañnan wayar Kawu Sa'idu ya fada Masa yayi ta duka na Dan nasan zaiyi abinda yafi Haka. Ranar wata lahadi na tashi da zazzabi da azababben ciwo Ciki Wanda nasan Yunwa ce ta saka hakan, nayi kuka nayi juyin har bacci ya daukeni, se wajen asr na tashi nayi wanka sannan na fito Dan daura abinci, na samu shinkafar ba tafi gwangwani daya ba, na dafa sannan na zauna naci, Ina cikin ci naji muryar shi alamar Yana waya, ya shigo kitchen din ya tsaya Yana kallona, ko inda yake ban kalla ba na cigaba da cin abinci na, Yana tsaye Bai motsa ba yau a wuya nake Dan tunda na tashi a zazzabin na dauki alkawarin Rama duk abinda zaiyi min Koda zai kashe ni ne. Kamar yasan me nake tunani se ya fita daga kitchen din, na sauke ajiyar zuciya na Gama na fara wanke wanke se naji Yana kwalla min Kira, na duba kitchen din tas Ina neman makami, Idanuna Suka sauka akan set of knives da ban taba amfani dasu ba, na dauka butchers knife na zura cikin sleeve Dina na fito, yana tsaye Yana wurga min harara kamar idanun shi zasu sakko, na tsaya nesa dashi Ina Masa kallon tsana nace " Menene?" I swear seda Naga bakin shi ya bude saboda mamaki, ya nufo ni gadan gadan, na zaro wukar daga hannun riga ta, ya daga hannu shi zai mare ni nasa wukar na yanki damtsen shi sannan na wullar da wukar na tsaya Ina huci, hannun ya rike ya saki ihu, a take jini ya fara zuba, Dan na yanka tundaga rigar har jikin shi, nayi baya se daki na datse kofar Ina jin ihun shi, se naji me yasa ban ma kashe shi ba yadda idan yaso Nima se a kashe ni kowa ya huta, na Jima a tsaye se naji an bude gate an shigo daga baya na daina jin ihun shi, agogo na kalla Naga karfe hudu da rabi, jakata na dakko na ciro warpper 200 wadda mummy ta bani na saka katon hijab na dauki wayata na fito ba tareda na kulle dakin ba, Ina zuwa Naga saboda rikicewa a bude ya bar gidan, ga jini kacakaca tunda ga parlo har waje, na fice daga gidan na fara tafiya ba tareda nasan inda zanje ba, Ina zuwa Naga napep nace Tasha zai kaini zanje Kano, Ina Hawa ya kaini har lokacin nayi blocking duk wata channel din tunani a kwalkwalwata, Ina zuwa Tasha na samu mota baa Jima ba ta tashi se lokacin komai ya fara dawo mini, what if idan ya mutu kenan na kashe rai Zan mutu kafira, me yasa banyi hakuri an raba auren a hankali ba. Se na fara kuka Ina jin tsoro Yana ratsa ni, Ina ganin kamar kamani zaayi. Ta gefena se hakuri take bani tana lallashi na Dake datijuwa ce. Dake Babu nisa sosae se gashi mun so Kano, na kirga kudin na bashi sannan na samu guri na zauna Ina tunanin inda zanje, nasan Mummy Bata tafi ba, Amma sunyi tafiya kamar yadda Rooks tace min, su Ummiey basa nan, shi Kuma Kawu Tijjani bana son zuwa gurin shi Dan matsoraci be, se kawai na tuna uncle Babawo na saya airtime na saka na fara Kiran shi kowanne bugu na Kara bugun zuciyata! Seda na fitar da ran zai dauka sannan ya dauka " Princess!" Se na saki kuka jikina na rawa tamkar mazari, " Me ya faru? Ya akai? Kina Ina nake jin hayaniya?" Na kasa magana se kuka nake, gaba daya ya tada hankalin shi se roko na yake na fada masa menene, se can nace " Na kashe shi! Nasan kasheni zaayi!!" " Junaidun?" Ba gyada kaina, hankalin shi ya tashi yace na tsaya yanzun zai taho kazauren, se nace ai na baro kazaure Ina Tasha a Kano, Allah ya taimaka shima Yana kanon yace Yana Hanya na jira shi! AFIYYA is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment to 09063467258.39 Koda alkawarin da sukai min Basu cika ba,wannan Abu daya da sukai min se naji duk wani haushin su day fushi da nake dasu ya yaye, ko Babu komai wannan lokacin shi ne hardest moment of my life, da ace Bai kawo min dauki ba sede nayi ta watangaririya a titi tunda nasan Babu Wanda zai kula Dani Kuma. Kawu Tijjani yayi min alamar naje daki akan zasu Yi magana, na kuwa Mike Ina jin tamkar anyi min bushara da aljanna na koma dakina, na samu Anty Nafisa tana jera min Kaya cikin wardrobe. Na Isa gareta nace "Ki kawo nayi Dan Allah!" Ta juyo ta harareni tace " Dama haushin ki nake ji.." Gabana ya fadi na marairaice fuska Ina jin to meye hakan Kuma "... Wai Kika tashi da sassafe ki kafa shara da wanke wanke bayan nace kiyi bacci da yawa" Na sauke ajiyar zuciya nayi tunanin nan dinma wani Abin Zan fuskanta Kuma, nayi murmushi nace " Kai Anty ni bazan iya Zama idle ba, bana komai. Lokacin Ina gidan su Yaya tun asuba nake fara aiki Kuma Haka nake yini Ina Yi, Kinga aiki ya zame min jikina" Dana fada sunan Yaya se na tuna dashi, Allah kenan komai cikin tsari yake tsara shi. " To Banda abin ki ai nan ba gidan Yaya Sa'idu bane gidan favorite Uncle din ki ne, kede ki huta da kyau Dan zai fara nema Miki admission ba dadewa ba" Na Kara gyara zamana nace " To Anty waec din ya fito ne?" Tace " Ya fito Mana, printout din ki na gurin Darling bara ya Gama ya Baki, bakiga yadda Kika ci ba" Na saki hamdala Ina murmushi me kyau na Jin Dadi, Ina nan zaune ta Gama gyarawa tas sannan ta zauna gefena tareda bani jaka tace min " Kinsan me yasa wanann abubuwan duka Suka faru? Kunyi sakaci da addua dukkan ku daga ke har su Darling din bakwa addua, Dan Haka yanzun addaua zakiyi sosae, duk dare Zan dinga zuwa Ina tashin ki kiyi sallah ki roki Allah mafita, this is not the end of it har yanzun akwai aurenki akan Junaidu" Na gyada kaina tabbas hakane, addua mukai sakaci da ita shiyasa abubuwa da dama suka lalace cikin rayuwata, dukda nasan kaddara akace ta riga fata Amma wani lokacin na kanji bamu ma fahimci concept din kaddarar ba, it's prewritten shiyasa akace muyi addua, wannan adduar can make a great change a cikin rayuwar mu, Idan da ace Babu abinda yake canja kaddara da bazaa ce muyi addua ba! JUNAIDU Kafin yankan da Afiyya ta ma Junaidu, cikin satin abubuwa da dama nashi suka fara lalacewa, a wañnan safiyar da ya fita, main source din kudin Junaidu wannan garage ne na gyaran motoci da Saida spare parts, se Kuma shaguna a jere guda biyar da yake dasu a Kano inda ya zuba Yan haya. Sauran duk yawancin kananan kadaru ne, Amma Kuma har lokacin Yana drug dealing dukda ba sosae ba kasancewar shi Bai fiya son risking safety din shi ba, Amma wani lokacin Safiyyu idan yaga chance Yana saka shi Dole se yayi tunda ba karamin kudi suke samu ba. Yana fitowa ya fara Kiran Safiyyu Dan sunyi akan zasu je asibiti saboda drugs din aka bashi akan matsalar shi sun Kare, Doctor yace Masa zai Sha maganin na kimanin sati kamar biyar kafin ya Kara gwadawa aga ko zaa dace dukda nerves din dake gurin anyi damaging dinsu sosae beyond repair! Safiyyu ya karaso Suka shiga mota Dan tafiya kamar yadda Suka shirya, se ga Kira a wayar Junaidu daga manager shi akan gobara baa San daga inda ta taso ba ta mamaye gaba daya garage din, Kuma ba guri daya ba ta barbazu ne cikin garage, a take Junaidu ya saki kara cikin tashin hankali yace " Ku Kuma Kuna me da har hakan ya faru? Dukiyata wallahi baa Isa ba!" Ya kalla Safiyyu da ya riga ya nufi inda garage yake can farkon gari kafin a kawo kanti, yace " Kaji Dan hauka sun bar gurin ya kone! Dukiyata, takama ta !!" Shi dai Safiyyu Bai ce Masa komai ba Dan Bai masan me zaice ba, suna Isa kafin ya Gama parking Junaidu ya fito a gigice yayi gurin da uban mutane suka taru kowa na tofa albarkacin bakin shi, Amma abun mamaki duk yadda suka taru Babu Wanda ya dauki Koda ruwa cikin kofi Dan ya kashe wutar, gaba daya sun zagaye gurin se Allah ya Kara suke wasu na fadin dama ai dukiyar jinin mutane ce dole zata kone kuwa. Ya ratsa ta cikin mutanen ya shiaga garage da already inda main heart din garage yake ta Jima da konewa, yayi wani ihu Yana kallon Safiyyu dake contacting fire service akan su kawo dauki, Junaidu Allah kadai yasan irin susucewar da yayi kafin zuwan Yan kwana kwana, Koda suka zo 3/4 na abinda yake ciki ya kone se gini Haka ya dinga faduwa yif Amma ko sauran da suke makwabtaka dashi wutar Bata taba ba. Safiyyu ya rike shi saboda fizge fizgen da yakeyi, mutane sunata binsa da Allah ya Kara sauran ma zasu kone sannu a hankali, da kyar Safiyyu ya tafi dashi daga gurin Amma ba karamin asara ya tafka ba, abin tashin hankalin ma shi ne akwai motocin mutane, Kuma yawancin mutane suna Kai Masa gyara ne ba Wai Dan wani Abu ba se Dan Babu karya sun kware wajen aikin su. Safiyyu ya kaishi gida ya samu ya kwantar dashi tareda karanta Masa wasu spells a take bacci ya dauke shi, Bai farka ba se wajen uku anan Safiyyu ya masa bayanin cewar ai akwai damuwa Dan matsawar Afiyya na rayuwar su Kuma Bai kusance ta ba to abubuwan shi da rayuwar shi Baki daya ta dakko hanyar tarwatsewa, cikin fushi ya nufo gida da nufin yayi ma Afiyya dukan da ko Bata mutu ba to se ta nakasa ko ta jigata, ni Kuma na fito da shirina Allah ya bani saa na yanke shi. Safiyyu already ya biyo bayan shi Dan yasan definitely zaiyi wani silly Abu ne tunda ranshi kuwan a bace yake, Yana shigowa ya dinga jin ihun shi, shi ne fa ya shigo ya dauke shi zuwa asibiti, fada Masa yake ya kulle gidan kada na gudu kafin ya dawo, yau se ya kashe ni yaga uban da ya tsaya min. Ba karamin jini ya zubar ba, Dan kafin su karasa har ya Suma, ana zuwa tunda case of assault ne yasa aka Kira police, yazo ya shaida komai sannan aka dinke gurin it was so deep Dan na taba Masa artery shiyasa bleeding din yayi yawa. Aka Kara Masa jini duk Safiyyu ke ta wannan Kai kawon kafin Kuma aka samu ya farfado, da furucin se ya kashe ni shi ne abinda ya fara fada, dan sandan da case din ke hannun shi ya dubi Safiyyu yace Yana son magana da Junaidu, Dole Safiyyu ya fita Yana nuna Mai alamar yasan me zai fada. " Waye ya yanke ka?' " Mata ta ce" " Kunyi fada ne?" Ya gyada Kai, Bai San dalili ba kawai bakin shi yace " Dukanta nake shi ne a kokarin kare kanta ta yanke ni har Haka" Shi kanshi Bai San me yasa ya kareni ba dukda a ganina ba kareni bane ba ai gaskiyar ce, Dana tsaya na Bari ya dakeni kamar yadda ya saba sede Kuma Rooks idan ta haihu ta tuna tana da Yar uwa me sunana tayimin Kara ta mayar da sunan! Dan sandan ya fadawa in charge din emergency unit din akan kada suyi discharging Safiyyu har se an sanar da nan police station din. AFIYYA is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment to 09063467258.40 Tunda na tashi Ina daki ban fito ba, se addua nake Allah yasa komai yazo karshe, tun karfe uku saura na tashi na dare shi ne har yanzun ban koma ba, Anty Nafisa tazo ta tasheni da kanta, seda na tashi taga nayi alwala na hau Kan salayya kafin ta koma dakin su, nayi sallah sosae cikin nutsuwa da Mika Kai, da saka ran cewar Allah ya riga ya karba addua ta. Ita ta koya min yadda ma zanyi adduar, nayiwa Allah kirari da dukkan kalmomin da suke nuna girma da Kuma rahma, nayi salatin annabi yadda Zan iya sannan nayi istigfar, abinda nake bukata ya biyo baya, iyaye na da sauran alumma. Nayi na Gama sannan na koma karatun kur'ani na Gama na Kara sallah zuwa lokacin alfijir ya keto nayi rakaatanul fajr sannan nayi sallah abuna. Na Jima Ina zaune nayi azkhar na karanta suratul Yasin sannan na fada tunanin yadda abin zai kasance, dukda ban taba jin nutsuwa da sanyi irin Wanda naji ba, Ashe Haka addua take? Se nake jin tamkar face to face nayi magana da Allah, I felt so much relieved, naji tamkar lokacin da nake rayuwa ni da Abbuna da Nanny, lokacin banida wata damuwa ko matsala, Amma kalleni at 16years I'm exposed into abinda wata Yar shekara arabain din Bata taba fuskanta ba. Na mike nayi wanka na gyara gadon na shirya cikin skirt da riga na shadda brown, kasancewar ni ba fara bace yasa kayan Suka min kyau sosae, sede da na kalleni se Naga ramar da nayi ta fito da yawa, na shafa wuyana Ina turo bakina alamar rashin jin Dadi Amma dukda Haka na danyi kyan gani akan shekaranjiya. Knocking naji softly jikin kofar hakan yasa na dubi kofar se naji sallamar Anty, ta shigo har lokacin kayan bacci ne jikinta Bata cire ba se Dan veil data daura akai, ganina na shirya fes Dani yasa ta saki murmushi tana fadin " Kinyi kyau Princess din Darling" Nayi murmushi me kyau na gaishe ta ta amsa " Muje kitchen ko?" Na gyada Kai Ina tambayar ta ko Uncle ya tashi, tace ai tun asuba Bai ma shigo ba da yaje masjid se yanzun ya kirata akan Yana shigowa kazaure zasu wuce, na gyada kaina. Kusan karfin hada breakfast dinma ni ce, tunda ita ba ta da sauri, mun kusa gamawa mukaji sallamar uncle Babawo ya dawo, da sauri ta dauki towel ta goge hannunta sannan tace min bari ta ganshi, na gyada Kai Ina murmushi, a raina nace she's so lucky tana zaune cikin farin ciki. Hanzarta gamawa nayi na fito bayan ba Dan gyara gurin na same su zaune suna magana, Yana kallona ya saki murmushi Yana fadin " Princess har kin tashi?" Nayi murmushi na karasa na gaishe shi, ya amsa da faraar da Yana Kuma bani reassuring look, a gurin mukai breakfast Yana bani labarin then lokacin Yana karatu a Lancaster Banda dariya Babu abinda nake, saboda yadda labarin yake so funny, gaba daya Suka tsaya suna kallona, ganin sunyi shiru yasa na tsagaita dariyar Ina murmushi na cigaba da tauna plantain din dake bakina, Anty Nafisa tace " It's nice seeing you smiling again!" Na Kara sakin murmushi bance komai ba, uncle Babawo ya wuce Dan yin wanka, ni da Anty muka kwashe kayan muka gyara tsaf kafin muka fara Hira, me aikin ta na ta gyara gidan. Kamar daga sama naji sallama kofar parlor, wata irin mummunar faduwar gaba ce ta ziyar ce ni, nayi saurin mikewa hannuna har rawa yakeyi, ta kalleni sannan ta dubi kofar daidai shigowar Kawu Sa'idu afijajan, na kalleshi kamar yadda yake kallona, Anty Nafisa tayi saurin zura hijab din da take ajewa standby tana kallon shi Wanda shi Kam duk hankalin shi Yana kaina, ta rike hannuna tana kallon shi tace " Yaya sannu da zuwa" Ya karaso cikin parlon ya Kai hannun shi zai riko hannuna nayi saurin komawa bayan Anty Nafisa Ina kankame ta, ya saki hannun ya bude baki zaiyi magana se mukaji fitowar Uncle daga daki, nayi saurin sakin Anty Nafisa na koma bayan shi Ina rike hannun shi, Ido cikin Ido suke kallon juna, Uncle ya riko hannuna ya dawo Dani gefen shi yace " Sannu da zuwa, dama yanzun nake son zuwa gida na sameka" Ya dube shi yace " Dama tana nan? Dama Kai ka boye ta kenan? Kasan me tayi?" " Na sani ta sare shi a hannu, ya Suma an Kara Masa pint of blood, Amma kasan me? Naso kashe shi tayi. Ba boye ta nayi ba ta dawo gidan ubanta ne kuma no Zan kwatar Mata yancin da ka tauye Mata" " Babawo ni kake fadawa Haka?" " Na fada maka, I'm ashamed to call you a brother, you're a failure. Ka sani da na Gama dashi Zan dawo kanka, you don't have to waste your time coming, I'll come for you. Princess jeki daki" Na saki hannun shi na nufi dakin a guje Anty Nafisa ta bi bayana, sun Jima Ina jin cecekucen su Amma saboda tashin hankali da nake ciki na kasa fahimtar abinda suke fada. Anty Nafisa ta sa nata nanata addua " Allahumma la sahla illa ma ja'altahu sahla..." Se naji uneasiness din Yana sauka. Uncle Babawo ya leko yace mu fito zai sauke mu gidan Mummy, Dan Bai son barina anan Baki daya, har mun fito yace na koma na sako hijab Dani zaa tafi kazauren Dan ayu komai ya Kare, a cikin motar shi muka tafi, mukai branching muka dauki Mummy, se lokacin Naga Rooks, tana ganina ta taho Mummy ta dalla Mata harara tace " Ai na raba wannan kawancen, Babu ke Babu ita, she's a bad friend!" Nayi shiru jikina a sanyaye, ita Kuma ta fara kuka tana fadin "Uncle kana jin ta ko? Ka Bata hakuri Dan Allah. Wallahi Afeey tace Kar na fadawa kowa" Mummy kamar ita take wa magana tace " Zanci ubanki a gurinnan, da ta fada Miki tace karki fada Mana ke mahaukaciya ce! Baki San she's indirectly telling you she needs assistance ba. Zaki sani" Ta rike hannunta tana ta kuka, nayi saurin cewa "Mummy wallahi..." " Zan mareki a gurinnan! Kin zata na kyaleki ne? Ina son komai yayi burning down ne Zan dawo kanki kinji" Uncle Yana dariya ganin nayi shiru tareda rike hannun. Shi, yace Rooks ta dakko hijab mu tafi, Mummy ta watsa Masa harara ta karba key din hannun sa ta fice, seda muka jira ta dakko sannan muka fito Uncle nace Mana " Ku kyaleta zata sakko da kanta, she's a bully tun muna yara" Rooks ta saki dariya tana Kara goge hawayen ta, ni Kam murmushi kawai nayi muna Isa, har ta tada motar, yayi saluting dinta Yana murmushi ta Harare shi, tana kallona tace " Daughter zo nan ki zauna" Gefenta na bude na Shiga na zauna su Kuma suka shiga baya abin su, kallon time tayi ta fara complain din min kusa makara hakan yasa tunda ta hau titi take gudu, yayinda suke Hira itada uncle dake fada Mata yadda sukai shida Kawu Sa'idu dazun, tace how she wish gidan ta yazo da se ta kwada Masa Abu akai. In less than an hour min shigo Kano, main office din hisba muka wuce, nan muka tarar da Kawu Tijjani yana jirna mu, muka gaida shi sannan muka shiga ciki, commander muka samu Dan time din baa fara hisba a jigawa ba, already jiya Uncle da Kawu Tijjani sun filing musu komai, nan aka Kara min tambayoyi na fada yadda komai ya faru. Sukai filing sannan muka wuce kazaure, kafin muje already Kawu Sa'idu ya riga mu zuwa tuni Kuma har yasa an tura case of attempted murder zuwa capital Dutse gadawur! Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment to 0906346725841 Gaba daya na kasa gane abinda yake faruwa, already komai anyi documenting akan na yanke shi ne saboda Kare kaina akan Yana duka na, se Kuma report din da aka bayar a asibiti na yanke shi a hannu, Amma da muka je dutse se muka ga it's a total different case, ance na yanke shi a cikin shi har na taba internal organs dinsa, Haka Kuma ba Kare kaina nakeyi ba. I was so confused har jiri nake ji Bayan sun Gama magana da Kuma charges din da aka daura min. Gaba daya bani kadai ba hatta uncle Babawo kawai kallon Kawu Sa'idu yake, irin dama you're this bad? Shi Kuma se murmushi yake Yana kallon mu irin na cin nasara dinnan, Zama nayi saboda na kasa tuna yadda akai akai murde wannan abin. Uncle Babawo ya fito shida rep din hisba da Kuma Kawu Tijjani, sun Jima a waje kafin Uncle Babawo ya dawo ya samu dpo din yace Masa shi Bai yarda da wannan report din ba, Dan Yana da tabbacin anyi tempering dashi, sannan ya kamata aje can kazauren anyi investigating shi kan shi Junaidu, station din da har zasu iya canja report da asibitin. DPO ya kalle shi yace Yana shigar Masa aiki, ni I'm under arrest har se sun Gama bincike sun Kai court! Gaba daya hankalin mu ya Kara tashi, uncle Babawo ya dubi Mummy yace " Ki Kira baban Rooks yayiwa IG magana!" Wani lokacin ka kalla mutum ka kyale shi ne, baka San shi waye ba, ko Kuma idan Yana bacci kada ka tada shi saboda baka San idan ya tashi me zai iya Yi ba. Gaba daya a tsorace nake idan na kalla cell dinnan se naji zuciyata kamar zata fito, ban taba ganin irin wannan rashin adalcin ba, da zarar zanyi magana se ya hanani yace ai report din says it all, hatta report din da aka kawo daga hisbah board Bai karba ba, yace ai munyi tempering dashi. Har maghrib muna gurin, mummy da dukkan su se waya suke Yi. Wajen bakwai se muka ji sirene, lokacin an kawo Mana abinci, se kuka nake naki naci Suma dake ba a nutse suke ba babu Wanda ya takura min akan se naci. Bansan waye yazo ba Amma Naga DPO din da sauran officers din suka sun fita waje sun kame, Babu jimawa suka dawo da commissioner of police na jigawa state Baki daya. seda yafi minti biyar a ciki sannan wani ya fito yace da mu mu Shiga, naji wani sanyi ya ratsa ni, I just hope Allah ya tura min savior. Muna Shiga muka same shi zaune kujerar da DPO yake dazun, yanzun Kam yana tsaye se muzurai yake, na kalleshi Ina tuna abubuwan da ya fada some few hours ago akan ko waye zaizo we anyi convicting dina, dama irinmu ne muke Hana society zaman lafiya, karama Dani har nasan na yanki wani. CP ya kalli Uncle Babawo ya Mika Masa hannu sukai musabaha Haka Suka da sauran kafin ya kalla rep din hisba ya fara Masa tambaya, ya Masa bayanin hade report da aka harhada. Yayi going through sannan ya dubi DPO yace " Me yasa wannan yake a hannun shi baka karba ba?" Yayi saluting dinsa jiki na rawa yace " Sir! It's contrary to karar da aka Aiko daga kazaure" Ya gyada Kai yace " Bani na kazauren" Hannun shi na rawa ya Mika Masa ya karba, Nan ma yayi going through sannan ya dubeni yace " Amina right?" Na gyada Kaina, na kwabe fuskata alamar kuka, se ya girgiza min kai yace " Kar kiyi kuka fada min shekarar ki nawa?" Ina hawaye tuni ya wanke min fuska ta, na fada Masa in the next few months zanyi shekara Sha shida, se yace na bashi labarin parent Dina, wannan labarin da nake bashi yasa muka Jima har na dai kuka, daga nan sequence of questions followed kowacce Ina amsawa iya gaskiya ta, har seda aka zo zancen auren, nan ma na fada Masa dukkan abinda ya faru har zuwa sarar shi da nayi. Ya jinjina Kai yace " Idan na samu akasin hakan fa?" Na Kara raurau da idanuna nace " Allah it's nothing but the truth!" Ya gyada Kai ya dubi uncle Babawo yace muje zuwa gobe zaa sake magana. A hankali naji sanyi ya ziyar ci raina, na rike hannun Uncle Ina Kara sakin kuka Wanda kowa yasan na relief ne. Seda CP ya wuce sannan muma muka wuce zuwa 3star hotel inda mukai booking daki. Kusan wannan Daren raba shi nayi Ina kaiwa Allah kukan, duk juyin da Mummy zatayi zata ganni akan sallayya hakan yasa ta sakko ta tada Rooks sukai joining Dina Dan yin sallar Suma. Ana yin assalatu mummy tace nayi wanka Dan idan nayi sallah na koma na danyi bacci, hakan nayi se 7am na tashi na saka Kaya muka fita, ni cikin mota nayi breakfast. Muna zuwa Babu jimawa se gashi DPO din Kazaure ya iso da Junaidu Wanda har lokacin Yana asibiti Basu sallame shi ba, hade da report din da sukai compiling da Kuma asalin officer da yayi handling case din a asibiti. Wannan shi ne dalilin da yasa idan akai assault ko accident ake cewa azo da police officer saboda legal backing, a karshe baka San wakake dealing da ba, yanzun da ace sunyi attending Haka Babu officer it will cost their work. Se takwas da rabi CP yazo lokacin Kawu Sa'idu ya iso see hura hanci yake Dan duk tunanin shi ko nace kamar yadda boka ya fada musu nasara tasu ce Amma idan sukai sake ta kubce musu it will lead to their downfalls! Dukkansu sun girgiza ganin CP da kanshi ke handling case din, ko sun manta waye Uncle Babawo ne? Jikin Kawu Sa'idu yayi sanyi Haka ma Safiyyu Wanda su sukai bypassing kazaure Suka shigo da sabuwar Kara Dutse, Akan Kazaure na kokarin rufe maganar, Bayan Haka Suka dauki kudi me yawan gaske Suka bawa DPO akan kada ma ya saurareni komai ya Zama a favor dinsu. To bayan mun bar Ringim mun tasar ma kazaure se Anty Nafisa ta Kira Uncle Babawo akan police officers sunzo Kama ni daga Dutse, wannan yasa muka juyo har mun wuce danbatta muka komo Dutse muka samu komai ya canja. CP ya karba report ya duba Wanda shi ne asalin report din da akai compiling lokacin da akai admitting Junaidu. Ran shi ya baci yasa aka Kai Junaidu asibiti Dan a duba shi a kawo Masa report, iri daya ne dai yanka ne dai a hannun shi na hagu. Anan aka Gama komai aka tura Kawu Sa'idu cikin cell shida Safiyyu, anan hisba tasa seda ya rubuta min saki biyu sannan aka wanke ni daga zargin da ake min yayin da shima aka tura shi rehabilitation home, Amma me Kuna ganin shikenan komai ya Kare? Wani abun Yana gaba! Yanzun ma aka fara! Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258.42 Shikam officer din ko nace DPO stripping dinsa akai daga uniform din shi aka bashi suspension, Amma dukda Haka se naji tausayin su nakeji, abin duka is simple Amma sun Yi complicating din shi gashi nan dukka yazo musu Babu dadi. Muna gamawa da division muka wuce asibiti, already Kawu Tijjani yayiwa wani resident Doctor abokin shi dake aiki anan shekoni magana, akan zamuzo nayi running test, tun daga Kan pregnancy test aka fara, aka min na HIV, hepatitis aka min scan da sauran abubuwan da zanyi benefiting, but dukka amsa daya ne non reactive. Naji Dadi naji Kuma sanyi a raina, naji duk duniya tamkar matsalolina sun Kare, Babu abinda ke fitowa daga karkashin zuciyata irin hamdala ga ubangiji, I was so proud ni musulma ce, nayi addua Allah Kuma ya amsa adduar tawa! Ya Kuma kawo min dauki. Se dare muka taho daga dutse muka dawo Ringim wajen Tara na dare. Dukka a gidan Uncle Babawo muka sauka, Ina Shiga Anty Nafisa ta rungume ni tana fadin " Congratulations my dear! Allah yasa hakan shi ne mafi alkhairi" Nayi murmushi Ina maida Mata martani nace Amin, Dan a raina fada nake ai hakan shi ne alkhairi na San. Dukka tare muka zauna muka ci abinci, sannan uncle ya fita dasu Rooks Dan komawa gidan su. Ya rage ni da Anty Nafisa da ta zauna tana fada min, tsugunne Bata Kare ba, yanzun rayuwata ta fara, kada na sake nayi Wasa da addua, kada Naga wannan abin anyi solving dinshi cikin sauki haka, to na dage sosae da ibada. Na Mata godiya sannan na tafi daki nayi wanka na dauki takkadar sakin bayan na saka kayan bacci na, a hankali na warware takaddar inda idanuna Suka sauka akan watsatsan rubutu, yadda kuka San gajiyayyen Likita ne yayi rubutun, I remembered lokacin da yake rubutawa sunana completely Bai sani ba, ya rubuta Afiyya, CP ya karba ya yaga yace se ya rubuta complete sunana Wanda hakan ya gagara se fada Masa akai ya rubuta, to Nima hakan take se a takkadar Naga Ashe sunan shi Junaidu Ibrahim. Na kalla Naga saki daya, biyu yayi min. Na runtse idanuna a hankali Ina Fadi cikin Raina " Abbuna! Your little princess is a divorcee now! Allah ya jikan ku Kai da Mama, Alhamdulillah da ba ku gan wannan bakin cikin ba. Allah nagode maka" Se hawaye ya fara tickling akan kumatuna a hankali, na zauna na saka kaina tsakiyar cinyoyina Ina sakin kukan da nasan na Kai limit bazai ruku ba Kuma, Dole se ya fito. Na Jima Ina kukan kafin na goge idanuna, na ninke takaddar na aje dan nasan ubana zau karba da safe, Ina Gama addua bacci me dadi ya daukeni, bacci Rahma ne wani lokacin idan ka yishi tamkar ka mutu ne ka bar duniyar, Dan kuwa ka bar dukkan wasu problems dinka behind Amma to some extent a wani baccin problems din will still hunt you! Washegari ban tashi da wuri ba, bama ni na tashi ba, hayaniyar da akeyi Wanda na tabbatar cikin parlon mu ne ita ce ta tashe ni, na tashi na zauna tareda kallon wayata da ta nuna min karfe Tara har da kusan rabi na safe, nayi mamaki irin wannan baccin da nayi, Wanda na manta rabon da nayi irin shi, tabbas I'm born again! Hayaniya sosae akeyi na sauka na shiga toilet na wanke fuskata da bakina sannan na dawo na saka hijab har kasa na nufi kofar, Ina kokarin budewa naji " Ai an fada min ance Kai kasa aka kulle shi! Idan ba Kai ba waye zai saka Dan uwan shi ya shiga kurkuku! Me yayi muku Kun takura Masa Kun Hana shi rawar gaban hantsi..." Muryar Ummaan su Yaya ce, kaji fitsararru! Tazo kenan akan maganar kulle Kawu Sa'idu da akai, na juya na cire hijabin na cire kayana Dan ita ce karshen matar da nake son gani a yanzun. Wanka nayi na shirya zuwa lokacin shiru kake ji Babu maganar tata. Na fito na samu Anty nata Kai kawo a parlor da kitchen da Kuma bedroom din su. Da faraa ta na gaishe ta ta amsa tana cewa " Yau kin Sha bacci! Darling yace Kar a tashe ki kiyi me isarki" Nayi Murmushin jin Dadi nace " Ai na tashi naji maman su Mino tazo se nayi wanka" Ta gyada kanta ba tareda tace komai ba, Nima ganin hakan yasa na wuce kitchen na taimaka Mata tana aikin. Mun Gama breakfast muna zaune muna kallo se naji sallamar Rooks da Basman Kawu Tijjani, na Mike tsaye suka shigo bakinsu dauke da sallama da murmushi ta karaso ciki, Basma ta rungume ni Dan min Jima bamu hadu ba, Rooks ta zauna seda suka gaisa da Anty tace Mata " Mummy tace Wai tana ta Kiran wayar ki, Kuma Anty Jidda tazo ke suke jira" Anty Nafisa tayi saurin mikewa ta Shiga daki, Babu jimawa ta fito ta Mana sallama akan sun wuce kazaure kwaso kayana. Kwanciya Basma tayi saboda kallon da ya dauke Mata hankali, ni da Rooks muka fara Hira " Kinsan duk abinda ya faru wallahi laifin su mummy ne, ni yanzun na daina ganin laifin Kawu" Nayi murmushi Dan Nima nasan hakane sakacin su ne ya kawo hakan nace " Ai ya riga da ya wuce, Kuma gashi dukka mun koyi wani Abu a cikin rayuwa" Ta gyada kanta. Daga nan muka cigaba da Hira take fada min sun kusa komawa NY Dan Daddy ya Kira Mummy yace Mata daga can office sun fara complain akan hutun da ta dauka yayi yawa. Har wajen laasar munata Hira se daga can Basma ta tashi akan Yunwa takeji. Kitchen muka shiga muka daura abinci, munayi Muna hira har muka Gama. Na juye cikin warmers tunda da yawa nayi nasan duka idan Suka dawo to nan zasu sauka. Basu Suka dawo ba se Bayan sallar ishai, Muna daki min shiga YouTube muna kallon latest videos. Ni na fara fitowa, idanuna ya sauka akan Nanny dake tsaye, na wullar da wayar hannuna Kan kujerar Dake gefena, na ruga inda nake tsaye na fada jikinta tareda kankame ta " Nanny!" " AFIYYA!!" Na Kara rungume ta Ina sakin murmushi me kayatarwa tundaga karkashin zuciyata, na nuna tsananin farin cikin da nake ciki. Mummy ta shigo da sauran Suka zauna suna kallon mu, na saketa sannan na rike hannun ta Ina fadin " Nanny yaushe kika zo? Amma ba Zaki tafi ba ko?" Ta gyada kanta, Uncle yace na kyaleta ta huta idan yaso idan munje kwanciya se muyi duk hirar da zamui. Mu ukun muka kawo abinci muka musu serving, cikin jin Dadi muka fara ci, se na tuna lokacin da dukka zamu hadu gidan Hajiya ayi ta Hira Muna Yara, lokacin Basma na Baby, se Anty jidda ta goya Mana ita, ni da Rooks mu ta fada wani lokacin Hajiya ta karbe ta tukun. Allah sarki rayuwa kenan, gashi har ya wuce se tashin labari. Bayan Tara gidan ya watse se mu hudu, Uncle ya kirani yace jibi zamu wuce Abuja zaayi min visa, passport Dina yayi expire zaayi renewing sabo sannan zamu wuce London Dan tuni ya fara nema min admission. Ya nuna min ya dawo min da Nanny Dan na Kara samun nutsuwa, yace na manta duk wani Abu da ya faru na fuskanci sabuwar rayuwar Dake jirana. Naji Dadi Dan Haka washegari duk ta tafi a parking da muke, dan kayana na Kazaure da kayan sawa kawai Suka dawo se trolleys Dina Amma furniture din dama sun tafi da masu siya, ana jirgewa aka siyar dasu aka saka kudin cikin account Dina. Da daddare kowa na daki, naji sallama a parlor na dubi Nanny da ta fara guangyadi nace " Nanny ki kwanta, ana sallama zanje na duba" Ta gyada kanta cikeda gamsuwa tace " To" Na dauki hijab Dina na fita parlon, daidai Anty ma ta leko tana cemin " Bakiyi bacci ba?" Na kalla agogon parlon nace " Takwas ne fa Anty, sallama naji shi ne na fito na duba" Ta gyada kanta na nufi kofar parlon inda na tarar da Yaya a tsaye shi da Hafsa, muna hada idanu da ita ta rungume ni tana fadin " Afiyya Ashe kin dawo?" Na gyada Mata kaina na Basu hanya su shigo, Yana ta kallona ko kiftawa bayayi nace " Yaya ka shigo Mana!" Ya saki ajiyar zuciya yace " Tohm!" Tare muka shigo parlon inda Anty ke tsaye suna gaisawa da Siyama, ganin harda Yaya tace Bari ta Kira Uncle, se Yaya ya girgiza Kai yace " Gurin Afiyya nazo" Anty ta gyada kanta Bayan ta min kallon da ni kadai na gane me take nufi sannan ta koma daki. Zama nayi nace " Me yasa Baku zo tun dazun ba" Ya shafa Kan shi yace " Ai Uncle Babawo yace Kuna parking zaku wuce gobe" Nayi murmushi nace " Eh inshallah" Se ya gyara Zama yace " Ina Miki farin ciki da cikin kankanin lokaci komai ya warware a cikin rayuwar ki, yanzun hankalina zai kwanta Dan nasan zakiyi rayuwa cikin aminci da alkhairi. Kiyi hakuri! Nasan an zalunce ki a gidan mu, Bai ma dace nazo gabanki Ina Baki hakuri ba, Amma nasan ke me hakuri ce Zaki yafe musu, sannan Zaki bamu wani chance mu Kara zame Miki cousins, Dan Allah Kar kiga kamar I'm selfish ko Zaki yiwa Uncle Babawo magana a fito Mana da Baban mu? Ummaah Bata bacci tana cikin tashin hankali, can you please do me that favor?" Na kalleshi Ina murmushi Wanda karkashin zuciyata tafasa kawai take, a raina ayyanawa nake har shi ya Isa ma yazo gabana Yana fada min Haka? Ya manta irin abinda iyayen shi su kayi min? Ya manta duka zagi, yunwa da suka saka ni a ciki? Duk wata se an bada kudin abincina Amma a Rana a naci abinci da yawa sau biyu ne a Rana, me yafi wannan? Duk shekara se an bada kudin makaranta tata Seda yayi amfani da kudin wajen biyan bokan Shi, ko ya manta ranar da nayi sneaking naje wajen sa na dawo iyayen shi su kace cikin shege nayi, yazo a gaban shi ake dukana aka kaini scan Amma ya kasa fitowa ya Kare ni! To me yayi saura Kuma? Me zaice min yanzun? Ina ganin bamu da wani abun fada a tsakanin mu. " Afiyya I'm so so...." " Don't be! Abinda bakai da ba yanzun ma idan kayi bashi da amfani. Ka sani iyayenka bazan taba yafe musu ba, ko na yafe musu Allah se ya Kama su da cin amanar maraya, Nabiyyu SAW yace ka shafa Kan maraya saboda zuciyar ka zatai taushi, Amma shi se ya sakani cikin tsananin kunci da masifa, to me zance kuma? Zaman shi a prison dokar kasa ya taka ba tawa ba, ni sakayya ta Baku fara ganin komai ba, I'm not that naive girl anymore, Kun nuna min cewar ya kamata na canja" Duk maganar nan da nake Hafsa ko a jikinta cake din da na kawo musu take munching abinta, taci ta dauka exotic din Dana kawo ta kurba abinta hankali kwance. " Afiyya baban mu kawun ki ne, a yanzun matsayin mahaifi yake a gurin ki..." " Amma..." Se nayi shiru kawai ban karasa abinda nayi niyyar fada ba, ganin hakan yace " Hannunka baya rubewa ka yanke ka zubar!" Nayi dariya nace " Haba?! Da alama baka taba zuwa asibiti ba, ka kalla yadda mutane suke zuwa willingly ake cire musu hannun su Dan su huta da azaba, balle ku da Babu wnai Abu Dan nayi cutting dinku down" Ina Gama fadar hakan na shafa fuskan Hafsa dake kallona, innocently, nace " Hafsisi Bari na dakko Miki Abu kinji?" Ta gyada kanta na koma ciki na dakko kayan da na riga na hada Dan ita sede Ina dawowa parlor na tarar sun tafi, na daga kafada ta na kulle parlon na koma dakina na samu Nanny ta Jima da bacci. Maimaikon bacci se kawai na dakko kur'ani nayi tilawa sannan na kwanta Ina tabbatar da nayi blocking dukkan channels din tunani na, ya kamata wannan abin su tsaya a Haka, Dole nayi bacci me dadi! Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam to First bank of Nigeria, send evidence of payment to 09063467258. Please can I have your prayers?43 Daga emirate council din Ringim suka kaimu Kano, tun sassafe muka kammalla breakfast da sauran abinda ba zaa rasa ba. Na kalla kaina jikin fuskar wayata idanuna da sukai can ciki duka sun fito, wannan unexplained ramar da nayi a fuska ta cike se abinda bazaa rasa ba, jikina ne dai nasan wannan se a hankali dukda shima ya fara karbar canjin. Na saki ajiyar zuciya Ina Kara nanata kalmar alhamdulillah, na sani ba wayo na bane ko dabara ta yasa na Zama Haka ba, yasa na fita hannun wancan azaaluman ba, Allah ne yayi miracle dinsa da Haka dukkan godiya a gareshi take. Hijab na saka na fito da wayata a hannu Ina gyara zaman sandal wedge din kafata. Nanny na zaune alamar ita ta kammalla, tare muka wuce can parking space inda already motar ke jiran mu. Har na Shiga se Naga Hafsa tamkar an jefo ta, Uncle Babawo ya dube ta Dan shi Bai riga ya shigo ba, ta gaishe shi da murnar ta, inata kallon ta she's so carefree, nasan yarinya ce Amma tasan dukkan abinda ke faruwa, but she chooses to act naive and neutral. Bayan ta gaisa da kowa ta karaso inda nake ta tambayeni zancen kayan jiya, se na maida hankalina Kan Anty Nafisa wadda ita na bawa akan tasan yadda zaayi a aika ma Hafsisi din. Anty Nafisa tace ta bayar zaa Kai Mata gida, se ta rungume kaina Dan fito dashi ta window a kunne na ta rada min " Kar ki yafe musu!" Nayi saurin janye kaina Ina dariya itama tana Taya ni, na gyada Mata Kai nace " Ki gaida Mino sosae, kice na tafi Amma idan na dawo har gidan ta zanzo" Daga Haka ta wuce mu Kuma muka dauki hanya, leaving behind my oppressed life! Na bude sabon shafi cikin rayuwata. I know it hard, kafin wancan shafin ya Kare zaka Sha wahala but Amma Dole dai zai Kare, to every hardship anyi Mana alkawarin ease, ni dai inada yakinin nawa ya karaso. Tunda muka shiga airport naji wani irin yanayi, naji tamkar Ina juyawa zanga mahaifina, na tuna lokacin da airport a gurina tamkar zuwa kasuwa ne, na kalla yadda a shekaru uku da doriya an Kara gyara airport din. Muka zauna har seda jirgin su Rooks ya tashi Bayan harda kukan rabuwar mu ni Kuma Ina dariya, bana tunanin as simple as rabuwa da Rooks zai saka ni kuka, da dai da ne nasan se nayi to Amma yanzun na fuskanci abubuwan da kwakwalwa ta Bata son tuna su! Muna landing a Abuja wannan yanayin ya Kara lullube ni, na damke hannun Nanny da itama yanayin ta ya canja, na Kuma San tabbas ta tuna Abbuna da Mama ne, na tsaya jikin wani popcorn stall inda anan Abbu ke siya min, mutumin Yana nan abin shi, ni Kuma Abbuna ya rasu! Se kawai na saki kuka me daci, dukkan su suka juyo suna kallona, uncle Babawo ya saki hannun Anty Nafisa ya karaso inda nake tsaye na rufe fuskata da hijab inata sheshekar kuka yace " Me ya faru? Me akai Miki?" Nace cikin kuka " Abbuna na tuna! Abbu..." Se naji ya saki ajiyar zuciya, Anty Nafisa ta hadani da jikinta tana nuna min it's ok Dan nayi kuka saboda tasan tuna shi nayi, Amma ya kamata duk lokacin da na tuna shi na Masa addua har Mama ma da bansan ta ba shi ne kawai abinda suke bukata daga gurina. Na gyada kaina Ina share hawayen nawa sannan muka cigaba da tafiya, Uncle nama Nanny fadan biye ni da tayi tana sharar kwalla. Tunda muka doso hanyar Gwarumfa kaina kamar zai cire Dan kallo, kowanne titi muka shiga se memories din gurin ya dawo min a Haka har muka Isa gidan Uncle dake cikin wani sabon estate. Su kadai suka Shiga no dashi kawai juyawa mukai zuwa embassy Dan mu fara neman visa din. Munje muka ciccike formalities sannan aka ce mu dawo washegari. A gajiye tikis muka fito daga embassy ya tambaye ni ko akwai abinda nake so na girgiza Masa Kai se kawai ya tsaya wani ice cream parlor ya karba min scoops da frosted cake. Muna zuwa gida na samu har sun Gama gyaran gidan ta Gama girki suna zaune suna Hira, tana jin sallamar mu ta mike ta rungumo uncle wannan aladar ta ce Babu ruwanta ko waye a guri kuwa, saboda yawanci tana da aladun westners kasancewar a cikin su ta tashi. Farkon zamana dasu kunya nakeji Amma a hankali Naga su Basu ma damu Dani ba se ya zamana I admire their love da suke ma junan su. Seda ta gama pecking dinsa kafin ta dawo kaina, na tura Baki Ina cire sandals din kafata nace " Ni Baki murnar ganina ba kenan" Me zasuyi Banda dariya, uncle ya wuce ciki suna gaisawa da Nanny dake dariyar wauta ta, Anty Nafisa na kokarin hugging dina na ture ta na wuce irin nayi fushi dinnan, ta Dan daga muryar ta tace " Darling kaga abinda ka jawo ko?" Shi dai dariya yake har lokacin ya wuce daki, na zauna na fara cin cake dina. Kwana biyar mukai a Abuja visa ta samu da komai da komai na Shirin tafiya. Da yamma na gama hada dinner, Ina fitowa na samu Anty ta nufi kitchen din, na tsaya tace " Princess din Darling, Wai Zaki iya tuna kawar ki ta garki?" Na gyada Kai na ta Yaya ma Zan manta childhood friend Dita Amina Abubakar Rogo. Se tace min yace na shirya su kaini muga ko tana nan. Aikuwa a guje na wuce daki, Dan Nanny seda ta min fadan Wai za taga ranar da zanyi hankali. Na tura Baki nace " Duk nutsuwa ta?" "Ke Kika sani. Ni Kam kin Kira mamarki Bintu?" Na girgiza nace Zan kirata idan na dawo Dan ranar ta kirani ban Kira ba kuma. Cikin sauri na shirya na fito das Dani Nanny ta Kara kwatanta musu gidan sannan muka wuce, se Naga hanyar na dawo min tiryan tiryan, har muka Isa kofar katon gate dinsu, muna parking na fito se Naga an bude gate alamar fita zaayi, katuwar mota Lexus me numfashi ta fito, se Kuma Naga anyi parking an bude kofar da sauri, kafin na Gama tantance komai naji an rungume ni tamkar zaa balla ni, dodon kunnena har amsawa yake Sabida ihun da takeyi. Se data Gama sannan ta sakeni tareda riko hannuna, anan na Kare Mata kallo sure Amina Abubakar Rogo ce, ta Zama budurwa sosae, tayi kiba dukkan jikin ta sun cika ba zaka taba comparing dinta Dani that's skinny ba Kuma har yanzun jikina is developing. " Amina Afiyya innanlillahi Ashe we're bound to meet again? Kawai kikai vanishing into thin air" Ina murmushi sosar da ya bayyana hakorana nace " Amina I've missed you!' Na rungume ta nima, lokacin Yan gidan su da nawa Suka fara gaisawa. Na saketa na gaida Mom da Dad da Basu manta ni ba se kannenta guda biyu. Itama ta gaida uncle da Anty. Babanta yace ai Kano zasu tafi yanzun saa mukai muka same su, yanzun flight dinsu baifi hour da wani Abu ba. Haka mukai exchanging contact nace Mata London Zan tafi kawai zamuyi magana. Ranar nayi farin ciki na Kuma Kara tabbatar da kokarin Uncle nasan ya dawo min da komai da na rasa, sede BAHAUSHE yace baa Bari a kwashe daidai. Muna Isa gida na cire kayana mukai dinner tun a table na ishi kowa da labarin Amina Abubakar Rogo, Amma Haka Suka dinga saurarao na seda na kware tukun kowa ya samu lafiya. Ina komawa daki na tadda call da wata Turkish number, jikina ya bani ko Ummiey ko Kuma Nads, hakan yasa na fara kokarin returning Kiran Amma se wani ya Kara shigowa nayi saurin dauka se kuwa naji muryar Ummiey " Congratulations daughter! Se jiya nake jin abinda ke faruwa wajen kawun ki, naji Dadi Ina fata yanzun Babu abinda ke damunki" Na fara gaishe ta sannan nace Mata Babu komai, ta Jima tana min nasiha tareda shiwa uncle albarka sannan ta bani Nads muka gaisa kamar nace Ina Yaya Shehu se na Bari kawai. A wañnan Daren se past 12 nayi bacci munata waya da chatting da Amina Abubakar wadda tuntuni sun Isa Kano, ta fada min yadda suka ta nema na har Ringim sukaje Basu San wanne family nake ba se juyawa sukai, na Bata labarin auren da akai min har da kukan ta. A kwana na goma muka nufi airport Dan wucewa Lancaster. Muna boarding flight din wayata ta fara ringing, Truecaller tayi identifying Kiran daga Istanbul ne sede ba Ummiey bace ba Kuma Nads bace. Na fara kokarin picking naji ana kowa ya maida wayar shi flight mode, ayi fastening seat belt, plane about to take off! AFIYYA is not free, pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258.45 Ko baiyi magana ba kasan Yana cikin farin ciki, a ganin shi a wañnan lokacin Ummiey ta Gama Masa komai duniya da lahira. He'll surely use the time perfectly. Yana fitowa sukai Karo da Daddy da shigowar shi kenan, ya Dan matsa Yana bawa Daddy hannu sukai musabaha, ya kalleshi yace " You seems happy what's the news?" Ya shafa Kan shi yace " Daddy sannu da zuwa" Ya bugi kafadar shi a hankali Yana murmushi yace " Sannu ya naka office din?" Yace " Alhamdulillah not bad" Daddy ya gyada Kai ya shige ciki Yana Masa fatan alkhairi, hannun shi ya dunkule In a fist yayi wani juyi tareda sakin murmushi yace " Yes!" Nads Dake tsaye duk abinda yake tana kallon shi, duk a su hudun ta fison Shehu saboda sun fi dasawa, halayen sui sunfi Mata, Dan Tasha fada race da aure ya hallata tsakanin su tabbas shi zata aura, Kuma se yazo yayi rashin Saar Nusaiba, Dan ita a ganin ta ba karamar rashin saa bace kace Wai zaka aura Nusaiba, ita kanta da take mace ba taga abin burgeea a tattare da ita ba. Ta matso ta Sha gaban shi tare da Mika Masa hannu tayi crossing kafafun ta, ya kalleta cikin rashin fahimta yace " What?" Ta turo Baki tana wani sly smile tace " Payment!" " For?" " Afeeys' contact na London!" Yayi dariya sosae har ta Bata Rai yace " It's already in my upstairs! Ummiey ta rigaki!" Ta buga kafarta tace " To ka biya na Mata magana ta saurareka Mana" Ta fada tana bin Bayan shi Dan Yana Gama fada Mata yayi hanyar parlor. Bai kulata ba har ya zauna gefen Sarki dake kallon su, ta zauna itama tare da riko hannun shi stubbornly tace " Dan Allah Mana!" Yace " Kin dame ni fa! Ki kyaleni" " To biyana kawai zakai nida Rooks mu kafa maka kujera" Ya Mike yace " Yaya Sarki just warn your sister ta isheni" Sarki ya dube su sannan yace " Da alama ka kusa tafiya London kenan?" Ya gyada Kai Yana Kara bude bakin shi saboda murmushi yace " Sure, gobe Dana fita Zan fara neman visa!" Ya gyada Kai yace " Take care of her, she's suffered a lot" Yace " Inshaaa Allah!" Satin mu biyu na fara fita zuwa makaranta, bamu da wani nisa sosae da famous University of Central Lancashire. Ranar Monday tun asuba Dana tashi dauki Bai bar ni na koma ba, nayi wanka sannan nayi sallah na fito parlor, kitchen na wuce Mom ta fada min abin breakfast Dan Haka na fara hadawa, banana pancakes ne se tea. Ina gamawa na Dan ci kadan na koma daki na Ciro wani black trouser na saka da farar top sannan na saka hula Bayan na taje gashin kaina, open abaya green na daura a saman na danyi buttoning dinta sannan na dauka books Dina da system na fito parlor. Lokacin duk sun fito Suma, na gaishe su Mom tace " Kinyi bacci kuwa?" Nayi dariya nace " Mom nayi fa! Me Kika gani?" Tace " Ai Na zata dauki ba zai barki ba" Lokacin Dad ya fito shima ya Gama Shirin, Bayan mu Gama gaisawa ta Masa serving pancakes na zauna saboda tare zamu fita dashi. Kara naji alamar shigowar message, na dauka thinking Nads ce jiya ta barmin message akan taji Yaya Shehu zai zo London, Dan Allah nace ya taho da ita, shi ne nace Mata yaushe zaizo, nayi missing din shi sosae. Ita Kuma da taga ko kula maganar su taho tare banyi ba se tayi fushi tace ba zata Kara updating dina ba. Nads rikici! Message din Yaya Hasher ne Yaya Hasher: Good morning beautiful! Ya Kika tashi? Nayi murmushi Ina Dan jin dadin beautiful din da ya kirani dashi Me: I'm fine alhamdulillah! Kai fa? Yaya Hasher: Ina son na ganki, ya zaayi? Nayi shiru Ina tunanin possible yadda zaayi mu hadu, were millions of kilometers away, se nace Me: kazo London Mana! Yaya Hasher: Kinsan se nabi protocols da yawa kafinnan and I want to see you now please" Na danyi shiru Ina tunanin how's that possible ya ganni yanzun kawai se nayi offing data ta na saki ajiyar zuciya, Dad na gamawa muka wuce se school. Bana tunanin a Nigeria akwai irin wannan hadaddiyar campus din, tundaga gate komai yayi kyau environment din is so conducive. Karfe takwas calss din mu ya fara, Ina zaune kusan a gaba, lecturer ya shigo kana kallon shi kasan bature ne, yayi introducing Kansa as Mr James zai dauke mu intro to human biology. Seda ya samu dukka mukai introducing kanmu, anan na gane akwai wani guy da Kuma wata Yan Nigeria. Sauran Kuma yawanci British dinne, se yan across su uku making us six. Kafin ya fita ya karba email address din mu akan zai tura Mana soft copy na lectures din. Bayan nan se muka je breakfast muka dawo mukai Use of English shima wani British dinne, nayi enjoying class din sannan muka Kara lecture daya Mika tashi. Ina fitowa ana laasar nayi sallah naji Ina jin Yunwa, Amma se na daure na Kira Dad nace na tashi yace shima Yana Hanya zai karaso mu wuce. Ina nan zaune yazo muka tafi Yana ta tambaya ta yadda school din take nace Masa ai da dadi, lecture ma Babu wuya. Da daddare duka an tura Mana lectures din da akai na ranar, na Shiga daki na bi ta Kai na gane komai sannan na kunna data Dita, kamar Yaya Hasher na jira Sega WhatsApp voice call din shi. Na saki ajiyar zuciya Ina ayyana ya fiye naci, na sliding tareda saka shi a speaker " Beautiful" Se na samu kaina da murmushi nace " Naam! Ina wuni?" Ya saki ajiyar zuciya I can hear him sigh in relief yace " Lafiya Lau, ya Dad and Mom?" Suka Suna lafiya na bashi amsa sannan ya fara complain wai nayi shunning dinsa, yace Yana son ganina Amma naki bashi dama " Yaya Hasher na baka option kazo London mu hadu, kace it's a bit of protocols. Ta Ina zaka ganni for goodness sake!" " Face time, zoom, WhatsApp video chat duka ai zasuyi favoring dina" Na danyi murmushi nace " Kaga ba laifi na bane Kaine baka making abin easier ba, da se kace let's use this" Mun Jima muna Hira dashi tun Ina jin bana enjoying maganar har na dawo na saki jiki sosae, seda Mom ta so Kirana akan zamuci abinci kafin na Masa sallama na tafi. AFIYYA is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment to 090634672547 Cikin kankanin lokaci muka Saba da Yaya Hasher sosae, muka Zama so close da kullum se na fada Masa yadda rana ta ta kasance. Amma duk wannan shakuwar kullum karkashin zuciyata Ina tunanin se yaushe Yaya Shehu zai zo, Dan tun ranar da Nads tace min zai zo gaba daya nake anticipating zuwan shi, kullum idan na dawo daga school to see na tambayi Nanny ko munyi Baki, a Haka har sati ya wuce kullum amsar tata daya ce Babu Wanda yazo, da farko tana tambayata wa nake expecting, se nayi murmushi nace Mata Babu kowa. Ranar muna chatting Bayan na dawo daga school da Yaya Harith nake tambayar shi su Yaya Shehu yace min, ai Yana nan Yana ta neman visa Bai samu ba da tuni sede kawai na ganshi anan Lancaster, for that moment se na Dan ji Dadi da ba fasa zuwan yayi ba, se Kuma na fara adduar Allah ya sa ya samu visar da wuri ya zo na ganshi. A bangaren karatuna munyi nisa, dake ni me naci ce I enjoyed every bit of it, bana Bari na tsani wani course, Dan nasan da zarar na tsana course din to I'm dead. Haka kulllum nake zuwa na dawo. Ranar Saturday na tashi Babu inda zanje dan banida class se tutorials da aka hada Mana, Kuma na tashi bana son zuwa, Haka na fito kamar ko yaushe duk weekend se na danyi relieving dinsu da aikin gidan. Ina zuwa kitchen na nufa na wanke hannuna sannan na fito da kayan da zanyi amfani dashi na saka apron na fara girki, Ina cikin Yi Nanny ta sameni, muka gaisa se kawai ta zauna muna Dan taba Hira " Har yanzun kawun ki na a kulle fa" " Eh Amma naji ranar Dad na waya Wai kamar zaa sake shi har sauran ma" " Su Junaidu kenan?" N gyada kaina nace " Haka naji yace Wai anyi reducing sentence dinsu" " Amma ke ya kike ji? Kinji ko irin haushi dinnan?" Na danyi murmushi Ina ciccire parsley nce " Haushin me Nanny? Ni kawai nasan ban yafe musu ba, cutata da sukai nasan Allah zai saka min Amma duk hukuncin da zaa musu a duniya bazan ji na gamsu ba" Se ta gyada kanta kawai se muka cigaba da Hira har na Gama, a lokacin Mom ta fito ni Kuma na shiga wanka, ta biyo ni daki lokacin Ina shiryawa, ta zauna bayan mun gaisa tace Ina fesa turare jikin " Yau Zaki fita ne?" Na girgiza Kai nace " A'a Mom Amma Zan fita zamuyi badminton da su Sheriffa" Ta gyada Kai tace " Then muje kiyi breakfast kafin Rana ta take ko?" Na Mike Ina gayara zaman hulata muka fita parlor, Dad already ya zauna har ya fara ci, Haka yake min duk lokacin da nayi girki yayi ta hyping dadin abincin kenan bama ya jira ayi serving dinsa yake serving kanshi da kanshi, Zama nayi na gaishe shi inata murmushi sannan na diba nawa a plate naci Ina gamawa na Mike Dan su sun zauna lovey dovey. Sallama na musu na dauki racket Dina na fice, gida biyu ya rabamu dasu Sheriffa, su din Yan Bangladesh ne, makarantar mu daya sede kowa da course din shi, kanwar ta Amna na samu jikin railer din su tana Wasa, tana hango ni ta taho da sauri tana min magana, Ina murmushi muka gaisa sannan muka shiga ciki na gaida baban su, Maman su ta fita strolling ita da brother din su, racket din ta ta dakko muka fita Bayan ta dakko Mana ruwa cikin katuwar water bottle da disposable cups guda biyu. Haka muka wuce nan a layin yake daga dayan tsallaken. Muna zuwa duk yawanci mutane sun fito wasu na volley, wasu basket wasu Kuma lawn tennis. Muma Babu dadewa muka fara wasan mu. Munfi awa munayi sannan na samu guri na zauna wasu set din Suka karba, na tsiyaya ruwa na fara Sha gumi na Kara keto min na zauna Ina tsane gumin da karamin towel, gashi na duk ya kwanta na Kan goshi na, wristwatch din hannuna na kalla Naga karfe Sha daya tayi, racket dina na dauka na ma Sheriffa da wasu na gurin sallama na karasa na tsallaka titi se gida, ban samu kowa a parlor ba na wuce dakina, Anan na samu Mom na maida min kayana da aka kawo daga guga, na Mata sannu sannan na wuce toilet nayi wanka. Ina fitowa tace min " Zakije tutorials din idan anjima?" Nace Mata " A'a Allah na gaji" Ta kalla agogo tace " No! Zaki je, ki huta zuwa anjima se ki wuce." Haka na hakura nayi sallar azahar na kwanta amma maimakon nayi bacci ko na danyi shiru se kawai na fara chatting a telegram, Yaya Hasher ne muka ta Hira yake fada min sunje maiduguri Shi da Anty. Na bashi sakon gaisuwa gurin ta sannan na koma Hira da Rooks dake bani labarin saurayin ta. A Haka uku tayi na dauki jotter da pen da wallet na shirya we schoool. Gaba daya tutorials din baayi awa biyu ba muka tashi. Haka na fito ni kadai kamar yadda na Saba, hat yanzun sede mu gaisa muyi magana a class Amma banida wata kawa ko aboki. Ina zuwa junction na samu bus da zatai wajen mu nayi boarding sannan na zauna, nayi shiru Ina ayyana Junaidu ko ya shiryu? Ko ya fara sallah? Na girgiza Kai Ina ayyana zai dauki lokaci me tsawo kafin ya dawo Hanya, Ina Masa fatan dai duk inda yake Allah ya shirye shi... Se Kuma wata zuciyar ta fara tuhuma ta Akan dalilin da zai sa ma na dinga tunanin Junaidu, a dukkan mutanen duniya na rasa wa Zan Yi tunani se shi. Na dan ja tsaki Wanda yasa gayen Dake gefena cemin " Are you ok?" "Yes I'm!" Na fada Ina Masa murmushi se shima ya mayar min na cigaba da kallon hanya, yaushe rabon Dana tashi naji kunci? Yaushe rabon da nayi kuka ? Na shafa fuskata Ina tuna irin Mari series of them da suka sauka akan ta Amma yanzun duk ya wuce sede hat yanzun idan na tuna se naji Babu dadi cikin Raina. Sauka nayi na Shiga layin mu a hankali nake tafiya Ina kallon yamma inda Rana ke kokarin faduwa, yayinda rays dinnan Suka kawata saman se garin yayi Dan ja, ga iska na kadawa a hankali wadda nake jinta har cikin Raina, a hanya na hadu da few of our neighbors muka gaisa sannan na karasa gida, lokacin an Shiga sallar maghrib Dad ma ya fita, Nima Ina gaida su Nanny na wuce dakina nayi alwala na tada sallah, bayan na idar na zauna Ina Dan duba abubuwa cikin abinda nayi jotting dazun. Seda aka Kira Isha nayi sallah sannan na fito na samu Mom na fito da abinci, na Taya ta sannan na hado plain tea na zauna na fara Sha a hanakla. Na dubeta tayi kyau cikin skirt da riga na material se t saka veil a saman kayan nace " Mom kinyi kyau, why are you on veil Kuma?" Tace " Munyi bako ne" Na gyada kaina tareda kallon kaina, baggy shirt ne jikina, se sleeveless top Ash da Dan rabbit yellow a gaban rigar, da Zan fito na saka BF jacket baka akai hakan yasa banma Yi kokarin komawa ciki na gyara ba, se na saki dankwalin Dana daure kaina dashi, hankalina na tattara na mayar Kan kallon da nake Yi a wata Indian Tasha, muryar Dad naji yayi sallama hakan yasa na juyo na Masa sannu da zuwa na maida kaina kan tv, wajen 10 minutes naji wata nutsatsiyar murya cikeda amo me dadin saurare tayi sallama, da farko shiru nayi seda naji Dad na fadin " Ka Gama wayar, zo mu fara cin abinci" A hankali kamar me tsoron kada na juya Naga ba Wanda nake tunanin bane ba, na juya adan dadare, shi dinne kuwa Yana kokarin Jan kujerar Dake facing ta Dad zai zauna, nayi saurin kankame mug din hannuna saboda kada ya Fadi daga hannuna, Yaya Shehu looking all charming, yayi kyau cikin brown trouser da long sleeve shirt baka, ya Kara haske yayi kyau na kin karawa, na saki murmushi lokacin da muka hada idanu dashi, na taho inda yake tsaye shi Bai zauna ba Bai Kuma dauke idanun shi a kaina ba, Mom ta karaso hannun ta dauke da salad data Ciro daga fridge ta zauna tana kallon mu, Bai zauna ba seda na zauna sannan nace " Yaya Shehu yaushe kazo?" Yayi murmushi Yana Kara kallona, I can see the extreme happiness dake ciki na ganin yadda rayuwata ta canja Baki daya. Mom tace " Afiyy shikenan Babu gaisuwa?" Na rufe fuskata da hannuna Ina Kara sakin murmushi, a kunyace na gaishe shi ya amsa sannan na zuba Masa abinci ni Kuma nai serving ma kaina salad. Lokaci lokaci se na kalleshi na saki ajiyar zuciya, he's here close to me, na kasa gane farin cikin da nake ciki! Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258.[28/01, 13:41] +227 98 36 59 34: 47 Cikin kankanin lokaci muka Saba da Yaya Hasher sosae, muka Zama so close da kullum se na fada Masa yadda rana ta ta kasance. Amma duk wannan shakuwar kullum karkashin zuciyata Ina tunanin se yaushe Yaya Shehu zai zo, Dan tun ranar da Nads tace min zai zo gaba daya nake anticipating zuwan shi, kullum idan na dawo daga school to see na tambayi Nanny ko munyi Baki, a Haka har sati ya wuce kullum amsar tata daya ce Babu Wanda yazo, da farko tana tambayata wa nake expecting, se nayi murmushi nace Mata Babu kowa. Ranar muna chatting Bayan na dawo daga school da Yaya Harith nake tambayar shi su Yaya Shehu yace min, ai Yana nan Yana ta neman visa Bai samu ba da tuni sede kawai na ganshi anan Lancaster, for that moment se na Dan ji Dadi da ba fasa zuwan yayi ba, se Kuma na fara adduar Allah ya sa ya samu visar da wuri ya zo na ganshi. A bangaren karatuna munyi nisa, dake ni me naci ce I enjoyed every bit of it, bana Bari na tsani wani course, Dan nasan da zarar na tsana course din to I'm dead. Haka kulllum nake zuwa na dawo. Ranar Saturday na tashi Babu inda zanje dan banida class se tutorials da aka hada Mana, Kuma na tashi bana son zuwa, Haka na fito kamar ko yaushe duk weekend se na danyi relieving dinsu da aikin gidan. Ina zuwa kitchen na nufa na wanke hannuna sannan na fito da kayan da zanyi amfani dashi na saka apron na fara girki, Ina cikin Yi Nanny ta sameni, muka gaisa se kawai ta zauna muna Dan taba Hira " Har yanzun kawun ki na a kulle fa" " Eh Amma naji ranar Dad na waya Wai kamar zaa sake shi har sauran ma" " Su Junaidu kenan?" N gyada kaina nace " Haka naji yace Wai anyi reducing sentence dinsu" " Amma ke ya kike ji? Kinji ko irin haushi dinnan?" Na danyi murmushi Ina ciccire parsley nce " Haushin me Nanny? Ni kawai nasan ban yafe musu ba, cutata da sukai nasan Allah zai saka min Amma duk hukuncin da zaa musu a duniya bazan ji na gamsu ba" Se ta gyada kanta kawai se muka cigaba da Hira har na Gama, a lokacin Mom ta fito ni Kuma na shiga wanka, ta biyo ni daki lokacin Ina shiryawa, ta zauna bayan mun gaisa tace Ina fesa turare jikin " Yau Zaki fita ne?" Na girgiza Kai nace " A'a Mom Amma Zan fita zamuyi badminton da su Sheriffa" Ta gyada Kai tace " Then muje kiyi breakfast kafin Rana ta take ko?" Na Mike Ina gayara zaman hulata muka fita parlor, Dad already ya zauna har ya fara ci, Haka yake min duk lokacin da nayi girki yayi ta hyping dadin abincin kenan bama ya jira ayi serving dinsa yake serving kanshi da kanshi, Zama nayi na gaishe shi inata murmushi sannan na diba nawa a plate naci Ina gamawa na Mike Dan su sun zauna lovey dovey. Sallama na musu na dauki racket Dina na fice, gida biyu ya rabamu dasu Sheriffa, su din Yan Bangladesh ne, makarantar mu daya sede kowa da course din shi, kanwar ta Amna na samu jikin railer din su tana Wasa, tana hango ni ta taho da sauri tana min magana, Ina murmushi muka gaisa sannan muka shiga ciki na gaida baban su, Maman su ta fita strolling ita da brother din su, racket din ta ta dakko muka fita Bayan ta dakko Mana ruwa cikin katuwar water bottle da disposable cups guda biyu. Haka muka wuce nan a layin yake daga dayan tsallaken. Muna zuwa duk yawanci mutane sun fito wasu na volley, wasu basket wasu Kuma lawn tennis. Muma Babu dadewa muka fara wasan mu. Munfi awa munayi sannan na samu guri na zauna wasu set din Suka karba, na tsiyaya ruwa na fara Sha gumi na Kara keto min na zauna Ina tsane gumin da karamin towel, gashi na duk ya kwanta na Kan goshi na, wristwatch din hannuna na kalla Naga karfe Sha daya tayi, racket dina na dauka na ma Sheriffa da wasu na gurin sallama na karasa na tsallaka titi se gida, ban samu kowa a parlor ba na wuce dakina, Anan na samu Mom na maida min kayana da aka kawo daga guga, na Mata sannu sannan na wuce toilet nayi wanka. Ina fitowa tace min " Zakije tutorials din idan anjima?" Nace Mata " A'a Allah na gaji" Ta kalla agogo tace " No! Zaki je, ki huta zuwa anjima se ki wuce." Haka na hakura nayi sallar azahar na kwanta amma maimakon nayi bacci ko na danyi shiru se kawai na fara chatting a telegram, Yaya Hasher ne muka ta Hira yake fada min sunje maiduguri Shi da Anty. Na bashi sakon gaisuwa gurin ta sannan na koma Hira da Rooks dake bani labarin saurayin ta. A Haka uku tayi na dauki jotter da pen da wallet na shirya we schoool. Gaba daya tutorials din baayi awa biyu ba muka tashi. Haka na fito ni kadai kamar yadda na Saba, hat yanzun sede mu gaisa muyi magana a class Amma banida wata kawa ko aboki. Ina zuwa junction na samu bus da zatai wajen mu nayi boarding sannan na zauna, nayi shiru Ina ayyana Junaidu ko ya shiryu? Ko ya fara sallah? Na girgiza Kai Ina ayyana zai dauki lokaci me tsawo kafin ya dawo Hanya, Ina Masa fatan dai duk inda yake Allah ya shirye shi... Se Kuma wata zuciyar ta fara tuhuma ta Akan dalilin da zai sa ma na dinga tunanin Junaidu, a dukkan mutanen duniya na rasa wa Zan Yi tunani se shi. Na dan ja tsaki Wanda yasa gayen Dake gefena cemin " Are you ok?" "Yes I'm!" Na fada Ina Masa murmushi se shima ya mayar min na cigaba da kallon hanya, yaushe rabon Dana tashi naji kunci? Yaushe rabon da nayi kuka ? Na shafa fuskata Ina tuna irin Mari series of them da suka sauka akan ta Amma yanzun duk ya wuce sede hat yanzun idan na tuna se naji Babu dadi cikin Raina. Sauka nayi na Shiga layin mu a hankali nake tafiya Ina kallon yamma inda Rana ke kokarin faduwa, yayinda rays dinnan Suka kawata saman se garin yayi Dan ja, ga iska na kadawa a hankali wadda nake jinta har cikin Raina, a hanya na hadu da few of our neighbors muka gaisa sannan na karasa gida, lokacin an Shiga sallar maghrib Dad ma ya fita, Nima Ina gaida su Nanny na wuce dakina nayi alwala na tada sallah, bayan na idar na zauna Ina Dan duba abubuwa cikin abinda nayi jotting dazun. Seda aka Kira Isha nayi sallah sannan na fito na samu Mom na fito da abinci, na Taya ta sannan na hado plain tea na zauna na fara Sha a hanakla. Na dubeta tayi kyau cikin skirt da riga na material se t saka veil a saman kayan nace " Mom kinyi kyau, why are you on veil Kuma?" Tace " Munyi bako ne" Na gyada kaina tareda kallon kaina, baggy shirt ne jikina, se sleeveless top Ash da Dan rabbit yellow a gaban rigar, da Zan fito na saka BF jacket baka akai hakan yasa banma Yi kokarin komawa ciki na gyara ba, se na saki dankwalin Dana daure kaina dashi, hankalina na tattara na mayar Kan kallon da nake Yi a wata Indian Tasha, muryar Dad naji yayi sallama hakan yasa na juyo na Masa sannu da zuwa na maida kaina kan tv, wajen 10 minutes naji wata nutsatsiyar murya cikeda amo me dadin saurare tayi sallama, da farko shiru nayi seda naji Dad na fadin " Ka Gama wayar, zo mu fara cin abinci" A hankali kamar me tsoron kada na juya Naga ba Wanda nake tunanin bane ba, na juya adan dadare, shi dinne kuwa Yana kokarin Jan kujerar Dake facing ta Dad zai zauna, nayi saurin kankame mug din hannuna saboda kada ya Fadi daga hannuna, Yaya Shehu looking all charming, yayi kyau cikin brown trouser da long sleeve shirt baka, ya Kara haske yayi kyau na kin karawa, na saki murmushi lokacin da muka hada idanu dashi, na taho inda yake tsaye shi Bai zauna ba Bai Kuma dauke idanun shi a kaina ba, Mom ta karaso hannun ta dauke da salad data Ciro daga fridge ta zauna tana kallon mu, Bai zauna ba seda na zauna sannan nace " Yaya Shehu yaushe kazo?" Yayi murmushi Yana Kara kallona, I can see the extreme happiness dake ciki na ganin yadda rayuwata ta canja Baki daya. Mom tace " Afiyy shikenan Babu gaisuwa?" Na rufe fuskata da hannuna Ina Kara sakin murmushi, a kunyace na gaishe shi ya amsa sannan na zuba Masa abinci ni Kuma nai serving ma kaina salad. Lokaci lokaci se na kalleshi na saki ajiyar zuciya, he's here close to me, na kasa gane farin cikin da nake ciki! Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258. [28/01, 13:41] +227 98 36 59 34: 48 Duk yadda dandanon abincin yayi min dadi Kan harshe na, se naji cikina Kuma ya cunkushe Haka na aje fork din hannuna na tareda daukar saviette na goge bakina da ita, kusan lokaci daya dukka suka dubeni, Dad yace min " Ya akai?" Na danyi murmushi nervously nace " Na koshi!" Mum ta dubi plate din da ko 1/4 banci ba tace " Ko wani abun kike so ki ci?" Na girgiza Kai na Ina murmushi nace " Kawai na koshi ne fa" Ba yadda zasuyi Haka suka kyaleni na sakko daga Kan dining din na wuce parlor, har na zauna se Kuma na fasa kawai na dauki wayata na nufi dakina, Ina shiga na lumshe idanuna hoton shi tar a cikin kaina, yaushe na fara jin hakan a gameda Yaya Shehu na ayyana cikin zuciyata. Wayata da na aje saman dressing mirror ta fara ringing, na karasa se naga WhatsApp voice call ne from Nigerian number, nayi swiping na dauka tareda saka wa a speaker, " Anty Amina Ina wuni" Nayi shiru Ina son na tuna Wanda ya taba Kirana da wannan sunan Anty Amina, kafin na amsa ko na tuna me Kiran nawa tace " Ambaby ce, kanwar Yaya Junaidu" Haka yake! Sau daya muka hadu Amma su Suka taba Kirana da Anty, na saki murmushi " Ambaby ya kike?" Tace " Lafiya Lau! Kika tafi Babu sallama mukai ta Neman number din ki dukka watannin nan se jiya na samu" Na danji Babu dadi Amma ta Ina Zan fara neman su, sau daya kawai muka hadu Suma Basu sake dawowa ba, dukda a ranar da na fara ganin su Suka nuna min kauna Nima naji Ina son su Amma dukda haka a ganina Neman su ba wani alfanu " Allah sarki! Abinne ya faru da sauri, ni kaina ban shirya tafiya ba" "Mu bamu masan abinda ya faru ba Anty Amina, kawai dai idan munje gidan se mu ta bugawa shiru, kowa na unguwar yace baya ganin Yaya ba Kuma a jin motsin ki, shi ne Malam ya nemi kawun ki se ya fada Masa abinda ya faru! Kiyi hakuri" Nayi dariyar hakurin da take bani, kamar ita tayimin laifin " Ai ya wuce Ambaby Allah ya kiyaye gaba" Ta amsa da Amin sannan na Bata sakon ta gaida su Malam, har Zan kashe tace " Anty Amina kin yafe masa?" Na danyi shiru Dan na fahimci was take nufi Junaidu ne, se kawai nace " Zanyi saving number dinki mu dinga gaisawa" Daga Haka na kashe wayar tareda runtse idanuna Ina jin kwalla ta cika min idanu da na rasa dalilin hakan, se na sunkuyar da kaina na saki kuka a hankali, Ina cikin sheshekar kukan naji an turo kofar, nayi saurin mikewa Ina saka edge din mayafina da nufin goge fuskata da tayi kacakaca da hawaye, Mom ta shigo I can see the disappointment a idanun ta, ta karaso a hankali na fara kokarin yin magana tayi beating Dina, yace min " Ki wanke fuskar ki kije parlor kuyi sallama da yayanki" Na gyada Kai na wuce toilet na barta anan a tsaye, Dana fito Bata dakin hakan yasa na dauki hijab din data fito min dashi alamar na saka kenan. Na saka na fito a hankali, suna tsatsaye se murmushi yake suna magana da Uncle, na karasa na tsaya gefen Mom da ke ta kallona da damuwa a fuskarta, na Dan saki murmushi kadan nace " Yaya!" Shima da murmushi a fuskar shi yace " Afiyya Ummiey na gaishe ki" " Ina amsawa" Dad ya Mika Masa hannu Yana fada Masa yazo very early muyi breakfast tare sannan ya kalla Mom ya Kara Mata godiya. Ya juya ya nufi kofar fita, Mom tayi min alamar nabi bayan shi, a kunyace na take Masa baya, a kofa na cin Masa Yana tsaye ya daga kanshi sama Yana kallon taurari da kamar an watsa su saboda yadda sukai fito far ga Kuma wata da yake a cike ya kawata samaniya. Ya dube ni yace " I'm so happy seeing you cikin wannan yanayin. How have you been?" Na Dan rausayar da kaina ba tareda na kalleshi ba Nima Ina kallon saman da yake kallo, a hankali iska me sanyi tana kadawa har hijabin jikina na swaying. " Alhamdulillah! Aiki kazo Yi ne?" Ya girgiza Kai sannan ya gyada Kuma, hakan yasa na kalleshi da alaman tambaya " Gurin ki nayi niyyar zuwa, I wanted coming to see you! Da nake daukan leave a office se suka hada ni da assignment Kuma" Nayi murmushi da yasa dimples Dina lotsawa nace " Thank you!" Ya gyada Kai yace " I should thank you Afiyya!" Na kalleshi Ina harde hannayena a kirjina nace " Saboda me?" " For being safe and sound! You don't know how much your happiness meant to me" " Yaya!" " Zan nuna Miki a hankali, I told you then Ina sonki, yanzun ma Haka Ina son ki Kuma ko nan gaba Zan cigaba da sonki, Zan baki lokaci for you to heal se kiga abinda kike bukata a rayuwar ki, kiyi karatu Zan zauna har tsawon sati biyu a garinnan tare da ke!" Nayi shiru Ina jin dukkan kalaman sa suna sauka cikin zuciyata, na dago na kalleshi, idanun shi masu haske Suka haske ni, na saki murmushi Ina boye fuskata cikin hannuna, ya karkato daidai fuskata har Ina jin numfashin shi a Kan hannuna yace " Should I take that as a go ahead?" Nayi dariya Ina matsawa gefe tareda cire hannayena nace " Ka tafi dare nayi fa!" Yayi shrugging kafada sannan yayi min waving ya wuce, Ina nan tsaye har ya fita ya samu cab ya tafi sannan na kulle kofar na shigo ciki, daki na na wuce Ina tura kofa na samu Mom na zaune gefen gado alamar tana jirana, duk yadda nake kokarin ganin na boye tsananin farin cikin da nake ciki Amma hakan ya gagara, na bude bakina nace " Mom Baki kwanta ba?" " Ina zaman jiranki ne" " Babu abinda ya sameni, kawia Ina kuka me saboda tuna rayuwar da nayi a baya" Ta taso ta rungume ni tace " Kibi abinda zuciyar ki take so, dukkan wani Abu da Kika zaba ki sani ni, Darling duka Muna tare dake. Kiyi addua sosae kinji?" Na gyada Kai nace " Mom thank you" " Sleep well Baby!" Ta shafa kaina sannan ta fita ta jamin kofa, na fada gado Ina tuna dukkan kalaman shi Zan nuna Miki a hankali, I told you then Ina sonki, yanzun ma Haka Ina son ki Kuma ko nan gaba Zan cigaba da sonki, Zan baki lokaci for you to heal se kiga abinda kike bukata a rayuwar ki, kiyi karatu Zan zauna har tsawon sati biyu a garinnan tare da ke! Safiyar alhamis ita ce ranar da aka dage sentence din su Junaidu, kowannen su a mabanbantan waje yake Dan Haka nan kowa daban suka fito, Junaidu ya fito hannun shi Babu komai, Dan baije da komai ba Haka ya fito sikau, Yana fitowa hasken Rana ya dalle shi se yaji tamkar wata sabuwar rayuwa ya fara, ya juya ya kalla gurin yayi tsaki Yana jin babbar failure da yayi shi ne sakin Afiyya da yayi, komai ya lalace saboda ita, shi kan shi hanyar da zai samu kudin zuwa kazaure ma case ne! Bai bar Kano se yamma Bayan yayi buge bugen shi ya samu kudin mota, Bayan maghrib ya karasa ya tsaya a daidai inda katon garage din shi ya kone, se fili da Yan bullulluka, ya saki ajiyar zuciya Dan Bai San ta Ina Kuma zai fara ba, komai ya lalace ya ayyana a ranshi, Dan Haka Dole ya Koma drug dealing din shi. Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment to 09063467258.49 " Wai me yasa baka sallah? Me yasa tunda nake zaune cikin gidannan tsawon watanni ban taba ganin ka kayi sallah ba? Kasan falalar sallah kuwa? Kasan abinda ya raba musulmi da kafiri shi ne barin sallah? Ta Yaya zaka tsaya a gaban Allah a bincika aikin ka aga Babu sallah a ciki, kasan kuwa duk ran da yake sallah ana zata Masa alkhairi..." Ya cigaba da tsayuwa zuciyar shi na bugawa cikin sauri Yana iya hango lokacin da karamin bakin ta yake motsawa a hankali, iya karfin ta tsakanin ta da Allah nasiha take Masa, ya tuna lokacin zuwa yayi ya iske inda take tsaye ya dauke ta da Mari, Wanda yasa a gigice ta dafe kuncinta tareda yin kasa da sauri Amma bakinta Bai rufu ba, Junaidu ya kalli hannun shi Wanda ya Yi amfani dasu wajen dukan ta, wajen Marin ta yadda ya tsangwama Mata, Bai San me yasa yake jin kamar shi din Wai missing din Afiyya yake ko Kuma Yana Jim maganar ta tana Shiga jikin shi ne. Tsaki yayi Yana fadin shi zuciyar shi batada wani lokacin soyayya ko tausayi, ko tausasawa! A ganin shi zuciyar shi is as hard as abinda ba zakai tunani ba. Ya kallo parlon da yayi kura, komai an dauke Babu wani digon kayan Afiyya da ya rage, Bai taba tunanin yarinyar na da wannan gatan ba may be he wouldn't have messed with her, she was so innocent wanne irin son duniya yasa ya hada Kai da Sa'idu ya cuceta ba. Ya safe kanshi Yana jin inama har yanzun tana nan, da tuni Jin motsin shi kawai tayi Koda zai kashe ta zata fito tace " Sannu da zuwa, za kaci abinci" Ba zata samu komai ba se kallon banza ko ma wani lokacin ya make ta. Yayi tsaki Yana jin tsananin haushin Kan shi na wani tunanin wata banza Afiyya. Dakin shi ya wuce komai Yana nan yadda yake Babu abinda aka taba Masa, wayar shi ya dakko wadda dama anan ya barta kafin fitar shi lokacin da Afiyya ta yanke shi, ya dauka ya cire sim dinsa sannan ya saka cikin wata Yar karama sede Babu cahaji cikin battery, ya jona kasancewar akwai wuta, kafin ya hau ya fara binciko hard substance da ya boye, su cocaine, weeds da ampoules na POD yasan idan ya fitar da wannan kayan ba karamin kudi zai z Samu ba, wucewa yayi ya dauki wayar ganin ta danyi abin kirki ya fara Kiran Jarma, Jarma dai abokin shi na yarinta Wanda aka Kore su tare daga makaranta. Babu jimawa Jarma ya dauka Yana fadin " Shege abokina ka samu fitowa kenan?" Junaidu yace " Ka Bari na dawo shekaran jiya, banida kudi se a account banida ATM Ian son a saya kayannan" Daga bangaren Jarma yayi dariya yace " Ai da nasan kana dasu tabbas da Zan balle gidan ka. Zan Aiko a karba da daddare Amma Zan Aiko maka kudin amfani anjima" Ya Masa godiya sannan ya hautsina Kan shi Yana daukar wata zundumemiyar laya Yana jujjuya wa, a hankali cikin Kan shi ya ji muryar Afiyya na cewa " Innanlillahi wa inna ilaihil rajiun!!! Tsafi kakeyi? Wannan shirka ne baa hada Allah da wani a wajen bauta..." Ya tuna ranar da shi ne ko ruwa ta fito Sha shima Bai sani ba, Yana cikin incantation dinsa se kuwan yaji faduwar Abu, Yana juyawa ya ganta a tsaye jikin ta kamar mazari saboda rawa, Amma saboda karfin Hali send tayi Masa magana. Ya yadda layar yana Kara cakuda Kan shi da hannu shi tareda buga kafa ya toshe kunnen shi, what the fuck! Me yasa yake tunanin waccan yarinyar da ya Kira da dabba on so many occasions. Kawu Sa'idu Kam gidan Kawu Tijjani yaje ya karba kudin mota, Dan Bai ma same shi a gida ba Kuma Anty Jidda ko fitowa batayi ba me gadi ta bawa kudin ya bashi, ya kalla dari biyar biyar guda uku a hannun shi, shi kenan abinda zaa bashi, wucewa yayi Yan kaba ya hau motar Ringim, tun a mota suka fara haduwa da mutanen da ya sani, kowa se kallon shi yake kadan ne ma suka Masa jaje amm yawancin kallon banza ke hada su se Kuma masu yada Masa magana. Shidai Bai Kara cewa komai ba babban burin shi yaje gida yaga ta Ina zai fara gyara abinda ya bata, yasan ba lallai komai ya koma in place ba Amma yanada yakinin boka yace Masa Afiyya ba zata Dara ko Ina ba daga Ringim, so Dole ya maida auren ta da Junaidu Dan ya samu abinda yake so. Haka ya cigaba da tunani har suka Isa, Bai ma bi ta Tasha ba se kawai ya samu napep ta Kai shi kofar gida, Hanson ya bashi ya wuce ciki, tun daga kofar gidan yake jin muryar kubra " Wallahi ba se anjima ba, yazunnnan ki tattara ki koma gidan mijin ki, Nima nan zaman umarni kawai nake, Amma Babu wadda zata kashe auren ta ta dawo gidannan, Nima naji da nauyin kaina" " Ummaah wallahi Allah Ummaah bazan iya cigaba da aurennan ba, Dan Allah ki barni, nayi tunanin nan gidan mu ne, nayi tunanin kowanne lokaci na dawo Ummaah zaku saurare ni, zaku tsaya kuji meye matsalata, wa nake dashi Bayan ku? Ummaah na gaji da aurennan bazan iya ba Kuma" Ummaan su ta Kara hayayyako Mata ba tareda Tama gane me Siyama ke fada ba, " Duk abinda zai faru, ko me ake Miki Dole ki hakura ki zauna, kowacce mace a gidan mijin ta hakuri take. Yanzun tashi ki fice min a gida" Siyama ta dinga kuka Wanda yasa jikin Kawu Sa'idu yayi sanyi, a hankali ya saka kanshi cikin gidan ba tareda yayi sallama ba, so gaba daya su biyun bama su lura da shigowar shi ba, seda Siyama ta mike tana share hawayen tana fadin " Ummaah Zan tafi..." Bata karasa ba ta ci Karo da Kawu, ta saki jakar hannun ta ta saki ihun kuka tareda durkusawa tace " Baba ka dawo!" Lokacin kubra ta hango shi, ta taho Babu wani Abu ta rungume shi, sede yadda yaga gidan ya canja tun daga kofar gida, maganganun su, yanayin kubra da ramar da tayi yasan suna cikin bakin talaucin da ya guda tun farko. Ina kwanciya bacci me dadin gaske ya dauke ni, I felt new and relieved. Se nake jin Kamar na fara sabuwar rayuwa ne, I felt so happy da a Banda mafarkin farin ciki Babu abinda nayi, I'm sure da cewar da zaa haska fuskata da zakaga murmushi ne kawai a kwance akai. Sallar asuba ta sa na tashi nayi sallah sannan nayi wanka, dakin Mom na wuce Dan nasan Dad na masallaci Bai dawo ba. Tana zaune har lokacin bata tashi akan sallaya ba. Na gaishe ta se kallona take tana murmushi nasan tana tunanin abinda ya sani farin ciki har Haka ne. Ban wani Jima ba na koma na dakina Ina tunanin abinda tace min " Yayanki zai Yi breakfast nan, bansan me yake so ba, Zan fito zuwa anjima se mu fara ko?" Na gyada Mata Kai, tana nuna min na tambaya me yake so hakan yasa na kunna data na fara chatting Nads up, ta dinga dariya jin tambayar da na mata, se ta fada min daga karshe. Tareda Mom mukai Gama, wajen tara Ina zaune a daki Nanny ta shigo tace nazo inji Mom, na kalla kaina yau atamfa na saka riga da skirt na daura dankwalin bayan na saka sweater a sama saboda sanyin da aka tashi dashi. Fuskata tayi fes se glowing take kamar Rana, na fito cikin nutsuwa da wayata a hannu Ina karbar korafin Yaya Hasher da yace nayi bacci jiya without even saying goodnight, yau na tashi ban ce Masa Good morning ba. Banyi replying ba saboda karasowa ta parlor, se na saka wayar a flight mode na zauna kujerar Dake kallon tashi, yeah shi fa Yaya Shehu ya karaso. Da murmushi fuskata nace " Good morning! How's London?" Yayi murmushi me kyau yace " Not bad Amma akwai sanyi" Na gyada Kai na Mike na nufi kitchen Dan Taya ta kawo abinci. Tare muka ci suna Dan Hira yayidan jefi jefi na Kan yi murmushi ko dariya. Bayan mun kammalla na kwashe kayan na Kai kitchen anan Mom ke cemin zasu fita itada Dad se yamma zasu dawo, Nima nayi changing my fita da Yaya Shehu na Dan nuna Masa gari. I'm sorry, Dan Allah kuyi hakuri my exams is starting on Monday Inshaaa Allah, shiaysa kuke jina shiru, I've lots of documents da ko budewa banyi ba. Amma inshallah zanyi typing 50th page tomorrow se Kuma na Gama exams. Thank you for understanding! Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment to 09063467258.[15/02, 23:10] +234 703 364 5886: 49 " Wai me yasa baka sallah? Me yasa tunda nake zaune cikin gidannan tsawon watanni ban taba ganin ka kayi sallah ba? Kasan falalar sallah kuwa? Kasan abinda ya raba musulmi da kafiri shi ne barin sallah? Ta Yaya zaka tsaya a gaban Allah a bincika aikin ka aga Babu sallah a ciki, kasan kuwa duk ran da yake sallah ana zata Masa alkhairi..." Ya cigaba da tsayuwa zuciyar shi na bugawa cikin sauri Yana iya hango lokacin da karamin bakin ta yake motsawa a hankali, iya karfin ta tsakanin ta da Allah nasiha take Masa, ya tuna lokacin zuwa yayi ya iske inda take tsaye ya dauke ta da Mari, Wanda yasa a gigice ta dafe kuncinta tareda yin kasa da sauri Amma bakinta Bai rufu ba, Junaidu ya kalli hannun shi Wanda ya Yi amfani dasu wajen dukan ta, wajen Marin ta yadda ya tsangwama Mata, Bai San me yasa yake jin kamar shi din Wai missing din Afiyya yake ko Kuma Yana Jim maganar ta tana Shiga jikin shi ne. Tsaki yayi Yana fadin shi zuciyar shi batada wani lokacin soyayya ko tausayi, ko tausasawa! A ganin shi zuciyar shi is as hard as abinda ba zakai tunani ba. Ya kallo parlon da yayi kura, komai an dauke Babu wani digon kayan Afiyya da ya rage, Bai taba tunanin yarinyar na da wannan gatan ba may be he wouldn't have messed with her, she was so innocent wanne irin son duniya yasa ya hada Kai da Sa'idu ya cuceta ba. Ya safe kanshi Yana jin inama har yanzun tana nan, da tuni Jin motsin shi kawai tayi Koda zai kashe ta zata fito tace " Sannu da zuwa, za kaci abinci" Ba zata samu komai ba se kallon banza ko ma wani lokacin ya make ta. Yayi tsaki Yana jin tsananin haushin Kan shi na wani tunanin wata banza Afiyya. Dakin shi ya wuce komai Yana nan yadda yake Babu abinda aka taba Masa, wayar shi ya dakko wadda dama anan ya barta kafin fitar shi lokacin da Afiyya ta yanke shi, ya dauka ya cire sim dinsa sannan ya saka cikin wata Yar karama sede Babu cahaji cikin battery, ya jona kasancewar akwai wuta, kafin ya hau ya fara binciko hard substance da ya boye, su cocaine, weeds da ampoules na POD yasan idan ya fitar da wannan kayan ba karamin kudi zai z Samu ba, wucewa yayi ya dauki wayar ganin ta danyi abin kirki ya fara Kiran Jarma, Jarma dai abokin shi na yarinta Wanda aka Kore su tare daga makaranta. Babu jimawa Jarma ya dauka Yana fadin " Shege abokina ka samu fitowa kenan?" Junaidu yace " Ka Bari na dawo shekaran jiya, banida kudi se a account banida ATM Ian son a saya kayannan" Daga bangaren Jarma yayi dariya yace " Ai da nasan kana dasu tabbas da Zan balle gidan ka. Zan Aiko a karba da daddare Amma Zan Aiko maka kudin amfani anjima" Ya Masa godiya sannan ya hautsina Kan shi Yana daukar wata zundumemiyar laya Yana jujjuya wa, a hankali cikin Kan shi ya ji muryar Afiyya na cewa " Innanlillahi wa inna ilaihil rajiun!!! Tsafi kakeyi? Wannan shirka ne baa hada Allah da wani a wajen bauta..." Ya tuna ranar da shi ne ko ruwa ta fito Sha shima Bai sani ba, Yana cikin incantation dinsa se kuwan yaji faduwar Abu, Yana juyawa ya ganta a tsaye jikin ta kamar mazari saboda rawa, Amma saboda karfin Hali send tayi Masa magana. Ya yadda layar yana Kara cakuda Kan shi da hannu shi tareda buga kafa ya toshe kunnen shi, what the fuck! Me yasa yake tunanin waccan yarinyar da ya Kira da dabba on so many occasions. Kawu Sa'idu Kam gidan Kawu Tijjani yaje ya karba kudin mota, Dan Bai ma same shi a gida ba Kuma Anty Jidda ko fitowa batayi ba me gadi ta bawa kudin ya bashi, ya kalla dari biyar biyar guda uku a hannun shi, shi kenan abinda zaa bashi, wucewa yayi Yan kaba ya hau motar Ringim, tun a mota suka fara haduwa da mutanen da ya sani, kowa se kallon shi yake kadan ne ma suka Masa jaje amm yawancin kallon banza ke hada su se Kuma masu yada Masa magana. Shidai Bai Kara cewa komai ba babban burin shi yaje gida yaga ta Ina zai fara gyara abinda ya bata, yasan ba lallai komai ya koma in place ba Amma yanada yakinin boka yace Masa Afiyya ba zata Dara ko Ina ba daga Ringim, so Dole ya maida auren ta da Junaidu Dan ya samu abinda yake so. Haka ya cigaba da tunani har suka Isa, Bai ma bi ta Tasha ba se kawai ya samu napep ta Kai shi kofar gida, Hanson ya bashi ya wuce ciki, tun daga kofar gidan yake jin muryar kubra " Wallahi ba se anjima ba, yazunnnan ki tattara ki koma gidan mijin ki, Nima nan zaman umarni kawai nake, Amma Babu wadda zata kashe auren ta ta dawo gidannan, Nima naji da nauyin kaina" " Ummaah wallahi Allah Ummaah bazan iya cigaba da aurennan ba, Dan Allah ki barni, nayi tunanin nan gidan mu ne, nayi tunanin kowanne lokaci na dawo Ummaah zaku saurare ni, zaku tsaya kuji meye matsalata, wa nake dashi Bayan ku? Ummaah na gaji da aurennan bazan iya ba Kuma" Ummaan su ta Kara hayayyako Mata ba tareda Tama gane me Siyama ke fada ba, " Duk abinda zai faru, ko me ake Miki Dole ki hakura ki zauna, kowacce mace a gidan mijin ta hakuri take. Yanzun tashi ki fice min a gida" Siyama ta dinga kuka Wanda yasa jikin Kawu Sa'idu yayi sanyi, a hankali ya saka kanshi cikin gidan ba tareda yayi sallama ba, so gaba daya su biyun bama su lura da shigowar shi ba, seda Siyama ta mike tana share hawayen tana fadin " Ummaah Zan tafi..." Bata karasa ba ta ci Karo da Kawu, ta saki jakar hannun ta ta saki ihun kuka tareda durkusawa tace " Baba ka dawo!" Lokacin kubra ta hango shi, ta taho Babu wani Abu ta rungume shi, sede yadda yaga gidan ya canja tun daga kofar gida, maganganun su, yanayin kubra da ramar da tayi yasan suna cikin bakin talaucin da ya guda tun farko. Ina kwanciya bacci me dadin gaske ya dauke ni, I felt new and relieved. Se nake jin Kamar na fara sabuwar rayuwa ne, I felt so happy da a Banda mafarkin farin ciki Babu abinda nayi, I'm sure da cewar da zaa haska fuskata da zakaga murmushi ne kawai a kwance akai. Sallar asuba ta sa na tashi nayi sallah sannan nayi wanka, dakin Mom na wuce Dan nasan Dad na masallaci Bai dawo ba. Tana zaune har lokacin bata tashi akan sallaya ba. Na gaishe ta se kallona take tana murmushi nasan tana tunanin abinda ya sani farin ciki har Haka ne. Ban wani Jima ba na koma na dakina Ina tunanin abinda tace min " Yayanki zai Yi breakfast nan, bansan me yake so ba, Zan fito zuwa anjima se mu fara ko?" Na gyada Mata Kai, tana nuna min na tambaya me yake so hakan yasa na kunna data na fara chatting Nads up, ta dinga dariya jin tambayar da na mata, se ta fada min daga karshe. Tareda Mom mukai Gama, wajen tara Ina zaune a daki Nanny ta shigo tace nazo inji Mom, na kalla kaina yau atamfa na saka riga da skirt na daura dankwalin bayan na saka sweater a sama saboda sanyin da aka tashi dashi. Fuskata tayi fes se glowing take kamar Rana, na fito cikin nutsuwa da wayata a hannu Ina karbar korafin Yaya Hasher da yace nayi bacci jiya without even saying goodnight, yau na tashi ban ce Masa Good morning ba. Banyi replying ba saboda karasowa ta parlor, se na saka wayar a flight mode na zauna kujerar Dake kallon tashi, yeah shi fa Yaya Shehu ya karaso. Da murmushi fuskata nace " Good morning! How's London?" Yayi murmushi me kyau yace " Not bad Amma akwai sanyi" Na gyada Kai na Mike na nufi kitchen Dan Taya ta kawo abinci. Tare muka ci suna Dan Hira yayidan jefi jefi na Kan yi murmushi ko dariya. Bayan mun kammalla na kwashe kayan na Kai kitchen anan Mom ke cemin zasu fita itada Dad se yamma zasu dawo, Nima nayi changing my fita da Yaya Shehu na Dan nuna Masa gari. I'm sorry, Dan Allah kuyi hakuri my exams is starting on Monday Inshaaa Allah, shiaysa kuke jina shiru, I've lots of documents da ko budewa banyi ba. Amma inshallah zanyi typing 50th page tomorrow se Kuma na Gama exams. Thank you for understanding! Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria, send evidence of payment to 09063467258. [15/02, 23:10] +234 703 364 5886: 50 Na Jima tsaye gaban wardrobe din nawa Ina tunanin abinda Zan saka, dama ta barni da atamfar jikina Amma nasan idan tasan da atamfa na fita se nasha fada. Haka nan na dakko black trouser da pink top na saka na taje gashina in a bun sannan na saka bakar hula. Socks na saka na dakko sabon sneakers Dina pink da ya kawo min jiya na saka, na fesa mist sannan na dakko katuwar jumper na saka na fito bayan na dauki wayata da credit card din da nake amfani dashi. Yana zaune shi da Nanny suna Hira, Ina rufe kofa dukkan hankalin su ya dawo kaina, Nanny nata murmushi ganin fitowa ta, yayin da shi Kuma ya zuba min idanun shi Yana kallo na lokaci zuwa lokaci Kuma se ya Dan lumshe idon shi, a hankali na tako inda suke na dube shi nace " Yaya muje?" Ya mike Yana sighing na dubi Nanny nace " Nanny se mun dawo na siyo Miki ice cream?" Ta harareni tare da fadin " Tsofe tsofe Dani me zanyi dashi, Allah ya kiyaye. Me Borno kada kuyi dare" Ya juyo Dan har yaje bakin kofar fita Yana murmushi yace " Inshaaa Allah Nanny" Daga nan ya fice Nanny ta dubeni tare da fadin " Wuce Mana se yankare Baki kike" Na turo bakina Ina juyawa na fice ba tareda na sake magana ba, Yana zaune a mazaunin driver Yana kallon wayar shi, cikin nutsuwa na bude side din shi na shiga, ya dago Kan shi daga Kan wayar yace " You look beautiful Damsel" Nayi murmushi Ina jin Dadi a raina Amma bance komai ba, ya tada engine sannan yayi reverse muka hau titi sannan ya fara magana cikin nutsuwa " Wanne course kike a school din?" Nace " Nursing nakeyi" " Why? Nursing is stressing" Na kalleshi Naga alamar zolaya a fuskar shi hakan yasa nace " Law ma ai is stressing" Yayi dariya wadda tasa na shagala kallon shi, ya Dan daki steer wheel din kadan yace " Kin Rama kenan? But can you do that tedious work?" Na danyi Jim nace " Zan iya" Yace " Ok! All the best then. Kinsan cewar I got your back ko? Komai Nene kike so Zan tsaya Miki, I just want you happy" Ina murmushi da ya fitarda hakorana na dube shi, I felt some gush of feelings cikin jinina, nace " Na sani and thank you" Ya girgiza Kai Yana kara maida Kan shi Kan titi yace " Meye na godiya, a husband should all this to his wife" Idanuna a warwaje nace " But you're not my husband ai" Yayi dariya tareda Kai hannun shi ya lakuce min hanci na yace " See you I'm trying to be, ai wannan Karan zaa bani chance ko?" Na gyada Kai na Ina murmushi Wanda ke saka min nutsuwa cikin Raina, ya gyada Kai tareda shafa kanshi yace " That's my Damsel" Daga Haka se mukai shiru, motar tayi shiru Nima na Dan lumshe idanuna tamkar me yin bacci Amma bashi nake ba Ina tunanin rayuwa ne da yadda take canjawa, Ina daukar rayuwa tamkar littafi Dake kunshe da chapters Wanda kowacce chapter baka San menene a ciki ba, se idan ka bude, farin ciki da bakin ciki Basu dawwamma Dole akwai canji Haka ma akai Mana alkawari, ba lalle rayuwa taxo maka yadda kake so ba ko Kuma yadda ka tsarata ba Amma Kuma lokuta da dama canjin idan yazo zai Faye maka alkhairi saboda Allah shi yasan menene kake bukata kaima kanka lalube kake a cikin duhu. Na saki ajiyar zuciya tare da bude idanuna jin yayi parking, se Naga min iso kofar wani katon mall ne, ya dubeni yace " Let's go in! Ke ace ki nuna min gari Amma Naga alamar ba inda Kika sani" Nayi murmushi nace " Itama Mom tasan fa ba inda na sani se school Amma tace Wai na rakaka" Yayi dariya tace " She wants us together shiyasa" Na Dan tabe baki nace " Idan bana so fa?" Se Naga ya tsaya da unbuckling seat belt dinsa yace " What? Me Kika ce?" Na juyar da kaina dayan bangaren Ina kallon yadda mutane ke zirga zirga a ciki da wajen mall din, ya saka hannun shi ya juyo da fuskata Dan na kalleshi, hakan yazo min a bazata na ture hannun shi, shima se ya sauke Amma still fuskar shi a Babu annuri but he looks Charming, exactly Ina kallon shi naji tamkar charm nayi saurin cewa " Nifa ba Haka nake nufi ba! Ni fa bana son kaga ko Zan soka Dan wani relationship we have, no I want to love you for who you are" Wannan Murmushin da yayi Yana kallona tamkar wani karamin yaro da ake Mika Masa alawa, he was so happy as I can see, nayi saurin bude kofar motar na fita Ina gyara moppler dake wuyana a zagaye, kaina a kasa Ina tuhumar kaina da sakin bakina har na fada Masa abinda na boye tuntuni nake tunanin Kuma yaushe Zan bayyana shi, but wannan Charming looks din nasa yasa na furta abinda banyi niyya ba. Nayi shiru har ya karaso ya kalleni Yana Murmushin da Bai bar fuskar shi ba yace " Muje Damsel!" Na gyada Kai har lokacin kaina a kasa yake, yayi dariya da tasa na kalle shi ya dage min girar shi, munyi yawo cikin mall din sosae na ware duk abinda na gani Ina so se na dauka takama ta na taho da credit card Dina, shima idan yaga girly Abu zai dauka nayi tunanin Nads yake Siyama seda muka je biya na Mika nawa credit card shima ya Mika nashi, na dubi cashier Dake kallon mu nace " Use mine please!" Hannun shi yasa ya karba nawan sannan Kuma ya bada nashi aka Mana packaging muka saka a mota, ya daukeni zuwa Bayan mall din Wanda yake kamar garden ga swings dasu wheels a gurin, kasancewar weekends ne couples da yawa da Kuma Yara sunzo gurin. Na hau Kan swing na kasa swinging seda yazo ta bayana ya tura ni sanann na fara Yi with full force, ya dawo gabana Yana min video,inata dariya tun karfina, har cikin zuciayta nake jin tsananin farin cikin da nake ciki. Se bayan laasar sannan muka fara kokarin komawa gida, Amma Kuma Ina Shiga mota Sega Kiran Aisha kawata, course mate Dita ce, na dauka muka gaisa tace min na zo school akwai tutorials da zaa fara in 10 minutes, na kalleshi dukkan hankalin shi na kaina, na girgiza Kai saboda na gaji ruwa kawai nake son naji a jikina dukda sanyin da ake ciki, na " Ba lallaii nazo ba gaskiya, kiyi min jotting down seki turon ko ta telegram ne please" Daga Haka mukai sallama, ya dubeni yace " Whatsup Damsel?" Cikin ko in kula na mashi bayani ya girgiza Kai yace " No you're going, muje na kaiki will wait for you har ki Gama kinji?" Ba yadda zanyi na gyada kaina muka dauki hanya, Babu jimawa muka Isa, tare dashi muka Shiga har venue din ya samu guri ya zauna, yayin da Aysha ke cemin " Kince da ba Zaki zo ba Kuma?" Na danyi murmushi nace " I changed my mind ne" Tace ai gwara da Kika zo, gurin shi naje nace Bari mu fara, ya min murmushi tare da dunkule hannun shi na bani courage na koma na zauna, duk inda na kalle shi se Naga ko dai Yana kallon wayar shi ko Kuma Yana kallona a Haka muka Gama sannan muka fito, Yana gaba Ina biye dashi se few of my friends da muka fito tare dasu. Aysha ta dubeni tace " That guy a Bayan class kamar ba Dan class dinmu ba ko?" Na gyada Kai nace " Tare muke dashi" Ta zaro idanun ta tace " OMG! Amina he's so cu.." Da sauri nayi cutting dinta Dan Kar ta Fadi abinda zanji haushin ta ko Kuma nan gaba taji kunya nace " He's my fiance, shi Zan aura idan mun Gama level 2. Muje ku gaisa" I can see kunyata a idanun ta, Naja hannun ta har sauran ma, Yana tsaye Bai shiga motar ba, nace " Honey! My friends" Ya dube su da fuskar shi wadda ke dauke da Murmushin kullum yace " Is nice meeting you! How's studies?" Duka suka amsa, ya dubeni inata murmushi Nima yace " I'm taking my Damsel away hope you don't mind?" Janet tayi dariya wadda kusan dukkan su dariyar suke tace ba karamin matching mukai ba, we look beautiful together, idan bazai damu ba zata Mana hoto. Na Dan matsa kusa dashi dukka hakoran mu a waje akai Mana, ta min waving wayar akan zata turon, mukai sallama sannan na shiga shima ya zagaya ya shiga ciki ya tada motar, a hankali yake tafiya tamkar a kafa muke tafiya yace " Da gaske after level 2 zamui aure?" Na dube shi da sauri nace " Ya akai kaji?" Ya nuna min kunnen shi Yana dariya, na dauke kaina yace " It will be coming soon kenan, na kusa Nima nayi owning abinda tunda na fara ganin shi ya hargitsa min lissafi, how will it be having you as my wife Damsel?" " It will be lovely ko?" Na fada Ina dariya ya girgiza Kai yace " Abu ne da ni kaina bansan yazan kwatanta shi ba, Ina fata komai yazo cikin sauki ko?" Na gyada Kai. Munata Hira har muka Isa gida, ya kashe motar ya fitar min da kayan sannan ya bani key din akan zaije yayi wanka ya dawo dinner, Ina tsaye har ya kule kafin na shigo ciki da Kaya Niki Niki, dakin Mom na Kai Dan har lokacin Basu dawo ba, kitchen najee na samu tana burabusko, na zauna bayan mun gaisa na hada coffee na Sha sannan na barta Dan hutawa kafin dare ya karasa Yi. _There goes my heart beating_ _Cuz you're the reason_ _I'm losing my sleeping_ _Please come back now_ _There goes my mind racing_ _And you're the reason_ _That I'm still breathing_ _I climbed every mountain_ _Swim every ocean,_ _Just to be with you_ _Fix what I've broken oh_ _Cuz I need you to see that you're the reason!_ Banbi ta Kan wayata ba seda nazo kwanciya, Ina Hawa WhatsApp Naga dukkan cousins Dina sun updating story dinsu, na Nads na fara dubawa tun kafin na bude Naga caption din " Love birds...let the feelings speak". Se ga hoton mu a garden ni dashi, na tsura ma fuskokin mu Idanu da suke fitar da annuri, you don't have to ask kinsan ba karamin so mukewa juna ba, na cigaba da dubawa har da aunties Dina ma sun daddaura, na fara kokarin duba nashi se na tuna ai banida contact din shi ma gaba daya. Na duba Rooks wadda tayi dogon sharhi akan picture din, yawanci tana nuna how much I meant to her, da Kuma adduar Allah yasa wannan shi ne farin cikin da kowa kemin adduar samu. Na kasa replying se kawai na koma chat Dina nan Naga messages, na Yaya Hasher Dake da yawa na fara dubawa, he sent me the picture da Kuma wani video lokacin munje wani guri da suke culture show, an bani Abu Ina kadawa Ina dariya yayi min video, a raina nace how on Earth abinnan ya fita Haka? Nasan shi ya daura kowa ya samu ya dauka ya daura, I'll be the hottest topic of gist kenan, tunda ba kowa yasan aurena ya mutu bama. Na sauke ajiyar zuciya na fara karanta messages dinsa *Dama shi ne dalilin da yasa Kika ki kulani yau kenan? You opened Chats Dina Amma Baki bani amsa ba, Wait tukunna meye tsakanin ki dashi? Do you want to rush again, yaushe auren ki ya mutu ko shekara bakiyi ba fa.* Na dafe kaina Ina jin kaina ya fara sarawa, Amma dukda Haka na cigaba da karanta na kusa dashi *Kinsan Ina son ki, kinsan da gaske nake son ki Amma ta Yaya Zaki ma soyayya ta Haka ta hanyar nunawa duniya Baki ma lura ba...* Ban karasa ba na aje wayar so confused... AFIYYA is not free, pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258. [15/02, 23:10] +234 703 364 5886: 51 Na dafe kaina Ina tunanin a yaushe ya nuna cewar Yana Sona da har zaice na nunawa duniya bani bukatar shi, na matsara da wayar gefe tare da furzar da iska daga bakina, yeah I actually know Yaya Hasher ya kula dani lokacin da nake cikin tsananin damuwa da matsala, lokacin da na ke bukatar Wanda zai kula Dani, Wanda Zan saka kaina Kan kafadar shi nayi kuka akai shi din ya zame min hakan,sede ko kadan ban kawo cewar Wai Yana Sona bane. Shiru nayi ba tareda nayi replying ba Dan ban ma San me zance Masa ba, a cikin zuciyata babu wani namiji da ke da matsayi irin na Yaya Shehu a raina, bazan taba manta abubuwan da yayi min ba, he was there for me when no one was there, he lend a helping hand, yaso kubutar Dani a lokacin da Wanda nake Kira iyayena Suka kasa min komai, Suka hakura suka made hannun su I remembered Bai hakura ba har seda yaga Babu yadda zaiyi sannan ya hakura, he kept telling me zai gudu Dani, ya Kuma nuna min na gani, bawai Ina returning favor din da yayi min ba, a'a zuciyata tayi naam da shi ta Kuma karbe shi hannu bibbiyu saboda shi din ya cancanci na soshi. Na numfasa na kashe data tareda kwantar da kaina Kan pillow a hankali Ina jin jikina Yana min Dadi Dan kowacce gaba ciwo take min, wayar na janyo jin alamar Kira Yana shigowa, na Dan tsirawa numbers din idanu kafin Kuma nayi sliding tareda karawa a kunnena, kafin nayi magana yace " Damsel" Take na fahimci shi ne, na saki murmushi jin nutsuwa tana Shiga ta, I felt kamar I'm safe a tare dashi, " Bakai bacci ba?" " Se kace ke wadda am sure yanzun kina Kan gado zakiyi bacci ko?" Na saki murmushi nace " How do you know? " Yayi dariya wadda naji ta har kaina, yace " Saboda Ina son ki! I can guess abinda kikeyi ta muryar ki. I can tell Koda numfashin ki ya canja, I can sense that!" Na gyada Kai kamar Yana gabana ina ayyana ok wannan shi ne ake Kira soul connection kenan. Tabbas souls dinmu are connected, mun Dan taba Hira inata Hamma yace " Awwww! Se yawning kike kamar Zaki hade ni. Oya sleep kinji?" Ba lumshe idanuna nace " To se yaushe zaka kwanta Kai Kuma?' " Immediately after na Gama tura mail dinnan kinji?" Na gyada Kai nace " Zakazo breakfast gobe?" " Noo Damsel zanje office da wuri am not sure idan Zan shigo" Se naji banji dadi ba, na Dan pouting lips dina nace " Ok then Good night" Yayi murmushi yace " I'm sorry, Zan so school da zarar na samu time. Sleep well Damsel" Daga Haka ya kashe wayar na kwanta Babu jimawa bacci ya daukeni ba tareda na kara tunawa da maganganun da Yaya Hasher yayi ba. Washegari da wurwuri na tashi Dan kuwa inada lecture da karfe takwas na safiya. Kitchen na shiga na daura tea sannan na fara hada noodles da prawns. Na Gama se zuwa lokacin Mom ta fito sanye da sleeping wears se katon veil data daura a sama, ta dubeni Ina zaune Ina kurban tea da wayata hannu Ina duba pharmacodynamics da pharmacokinetics saboda suna Dan rikita ni suke, Zama tayi na gaishe ta tace " Ya gajiya jiya Kun Sha yawo, I've seen pictures masu kyau har da videos" Nayi kasa da kaina, Ina sakin murmushi nace " Kai Mom" Ta danyi dariya tace " Feel free ni din nance fa, your friend. Kina son shi?" Na Dan dago Ina kallon ta ta gyada min Kai hakan yasa nace " Mhmm! Amma tsoro nakeji' Ta Dan kalleni da alamar tambaya tace " Tsoron me? Kada abinda ya faru ya maimaita Kan shi? My dear Inshaaa Allah Kim Gama kunci a duniya, ai Junaidu da Shehu mutane ne mabanbanta, hallayr su, dabiun su, wayewar su, sanin Allahn su. Da bakin ki Kika ce baya sallah, Wanda Bai Kare hakkin Allah ba ta Yaya zai Kare hakkin mutum? Shikam dai kinsan Shehu kinsan waye shi, tun ranar da na fara ganin ku tare naji how I wish shi din mijin ki ne to Amma akwai yadda Allah ya tsara komai, follow your heart and pray!" Na fahimci dukkan abinda take nufi Kuma Nima Ina jin hakan, na Dan langwabar da Kai nace " To Mom Yaya Hasher fa?" Kafin ta bani amsa muka ji fitowar Dad, ya karaso inda muke zaune ya tsaya daidai kanta Yana fadin " Me ake cewa Babu ni?" Mom ta dube shi ni Kuma na Mike Ina gaishe shi, ya amsa Yana murmushi yace " Princess Ina zakije? Kije ku karasa maganar ki" Na girgiza Kai nace " I'll be late to school" Daki na wuce bayan na leka kitchen na gaida Nanny sannan na wuce dakina na shirya na fito da backpack sabe a bayana, Dad na cin breakfast, Mom na zaune ta tattara dukkan hankalinta akan shi, da alamu magana suke me muhimmanci, na tsaya nace " Zan tafi" Mum ta dubeni tace " Wanne irin Zaki tafi, breakfast din fa?" Na yatsina fuska nace " I've took tea, se na dawo" Dad ya bani kudi sannan na juya na nufi kofar naji muryar Dad yace "Princess kinsan me yasa Yayanki Bai shigo ba?" Na juyo nace " Mhm! Dama zai je office ne shiyasa" Ya gyada Kai yace, " You call him for lunch ok? Kinsan saboda ke yazo garinnan ko?" Na gyada Kai Ina saka hannuna a baki kamar wata doluwa, Anty Nafisa tana murmushi tana Kara juya Masa tea din gaban shi " Treat him kindly he's your guest!" Nace " To Dad!" " Good girl!" Na juya Ina murmushi, a raina nace idan naki Yaya Shehu I'm sure yadda mutanen nan ke son shi akwai damuwa. Ba jimawa na Isa makaranta, mukai test akan pharmacology sannan na fito na kunna data ta ready to face Yaya Hasher. Aikuwa dai da sakon shi na fara cin Karo, hakan yasa na bude kafin na karanta Kiran shi ya shigo ta WhatsApp, na sauke ajiyar zuciya na dauka, muryar shi so down na gaishe shi ya amsa yace " Kin Gama guje gujen kenan?" Na Dan Bata Rai nace " Nifa ba gudu nake ba" " To me kikeyi? Tun yaushe na Miki magana Babu reply" " I was busy ne fa" Na fada straight away, yayi shiru har seda nayi tunanin bazai Kara cewa komai ba yace " Been busy Bai hanaki fita da Wanda kike so ba ko?" Na danyi tsaki siriri nace " Yaya Hasher let's stop this please, Yaya Shehu came all the way daga Istanbul to Lancaster, just for him to see me, kaga Dole Zan kashe komai nawa na bashi lokaci" " Saboda ni ban zo ba kenan. Amma kinsan Ina son ki ko?" Na girgiza Kai kamar Yana gabana nace " Bansani ba saboda you've never mentioned it" " But I showed you all the signs ko? Zakice Baki sani ba, Zaki nuna min Baki gane cewar Ina sonki ba" " Yaya Hasher kasan me? I'm thanking you for giving me your shoulders to cry on, bazan taba manta alkhairin ka ba, Amma Ina son kasan cewar nidin bansan kana sona ba saboda gaskiya bana daukar signs, for me to understand se idan mutum ya fada wannan kalmomin daga karkashin zuciyar shi zuwa bakin shi. Yaya Shehu ya fada tuntuni tun kafin nayi aure. We're just rekindling love din" Wata nannauyar ajiyar zuciya ya saki yace " Amina dama kina da Baki har Haka, what are you trying to tell me, kin zaba Shehu akaina? Just think about us mana" Nayi shiru kaina har ya fara ciwo, se nace Masa Zan Kira shi I need to eat, Ina aje wayar na dago kaina na gan shi tsaye akaina hannunsa cikin aljihun suit din jikin shi, he looks handsome wallahi, se naji kamar na boye shi kada wasu su kalleshi. Ya zauna gefena Yana sakar min murmushi yace " Whatsup? Waye yake Baki hard time a waya?" Na kalla wayar na kalleshi nace " Yunwa nake ji" Ya mike da sauri yace na wuce ya samo min abinci, tare muka ci sannan ya raka ni class ya tafi akan zamu hadu da daddare, da dukka ba zamu samu yin lunch a gida ba. AFIYYA is not free, pay 300 to3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258 [15/02, 23:10] +234 703 364 5886: 52 A hankali idanun shi Suka sauka akan mutanen dake zaune gaban massalaci, bawai a zazzaune suke ba, yawanci butoci ne a hannun su suna yin alwala kasancewar an Kira sallar laasar, ya kalle su ya dauke Kai tareda kokarin wucewa Amma se ya gagara wucewar, wani irin abu yaji a cikin zuciyar shi tare da amsa kuwwar maganganun Afiyya acikin kunnuwan shi, abin ya zame Masa tamkar wani nightmare, kowacce sallah idan aka Kira Yana zaune se ya dinga Jin tamkar wani nauyi cikin zuciyar shi. Ya karasa a hankali for the first time a abinda bazai taba tunawa ba ya dauki buta ya ciko da ruwa ya zauna a wani dakali can gefe ya fara alwala a hankali, kamar yadda yaga anayu, dukda Babu coordination Amma Yana yi din dai. Yana gamawa aka tada ikama Dan shiga sallah, wani farin Gaye a gefen shi ya Mika Masa hannu yace " Zaa Shiga fa" A hankali Junaidu ya saka hannun shi cikin na gayen suka shiga massalaci, wata irin nutsuwa yaji tana shigarshi, ya tsaya yaga yadda mutane ke ta hada sawu, suna jeranta kafafun su tareda hade duga dugunsu, se yaji zuciyar shi tayi taushi har danshi danshi ya fara bin fuskar shi, a karon farko ya fita " Astagfurillah!!!" Ya karasa a hankali ya jera da Yan uwan da musulinci ya hada dasu, suka tad sallah, kafin raka'o'i hudu su kammalu fuskar shi ta jike da hawaye, Bai taba jin wannan peace din cikin rayuwar shi ba kamar yadda yaji a wañnan lokacin. Aka idar kowa yayi addua ya fice, shi Kam kasa Koda tashi yayi se ya zauna ya cigaba da shiru da zurfi cikin tunani. Dama abinda ya Bari kenan? Dama Haka musulin ci yake d haske? Dama Haka sallar take da yayi neglecting iya rayuwar shi? Yana nan zaune har aka Kira mghrib, gaba daya yayi laushi ya taushi tubus, fuskar shi kawai zaka kalla kasan cewar akwai babban Abu a tare dashi, he looks pale and down, abubuwa sun Masa katutu kunya take ji Yana Kuma ganin tamkar dukkan zunuban shi a rubuta shi a Kan goshin sa shiyasa ya kasa daga idanun shi balle ya kalla wani. Yayi alwala yazo akai jamin maghrib,Bayan an Gama Malam wato limamin yazo ya fara nasihu kamar yadda yake duk Bayan sallar mgahrib da ishai, a wañnan ranar yayi nasiha Akan abinda ya Zama rampant rashin bin iyaye, ya dakko ayoyi da hadisai sahihai Wanda suke supporting dukkan bayanin shi, Wanda baibi iyaye ba to ya kamar Bai bi Manzon Allah SAW wanda baibi annabi ba kuwan yasan ya dakko gagurimin rikici tsakanin shi da Allah! Gaba daya jikin shi yayi sanyi tamkar an sassara Masa jiki Haka yakeji, a karshe yace shawara ce yake bawa dukkan mutanen dake sauraren shi indai har akwai rift tsakanin su day iyayen su to suje su daidaita tsakanin su tun kafin lokaci ya Kure musu. Kafin wani lokaci se tsiraru a cikin massalacin kowa ya Kama gaban shi, Haka nan ya cigaba da Zama har lokacin da akai sallar Isha wadda ya Kara yin nasiha akan zamantakewa da alumma, ya nuna cewar Allah yafi kowa sanin menene a zuciyar bawan shi Amma Dan ya nuna Mana muhimmancin exhibiting halaye masu kyau, shiyasa idan ka mutu se malaiku su dinga bin chamber chamber ta mutane suji shedar da zasu maka, Kuma wannan shedar zaayi amfani da ita wajen Yi maka hisabi, shiyasa idan ana maganar ka to ka dinga duba kanka, A known sociologist Charles Cooley yace looking Glass self, "The looking-glass self theory suggests that we come to know ourselves by reflecting on how others see us" Yadda kake daukar kanka ba lallai Haka kake ba, ya kamata kana duba ya mutane suke kallonka lokuta da dama shi ne ainahin yadda kake. Yana fitowa a massalacin ya samu napep, Yana Shiga me napep ya tambaye shi Ina zaije for unknown reason kawai yace a kaishi asalin gidan Malam, me napep ya kada napep se kofar gidan Malam, ya tsaya a kofar gidan Yana ganin irin mashahurin canjin da Suka samu, gidan Kan sjo ya canja, shekaru sun tafi Sha biyar tunda ya baro gidan Kuma Bai Kara komawa ba, ya tsaya Yana tuna lokacin yarinyar su day jamilu, lokacin da yake cin zalin yaran mutane, lokacin da ake Kai karar shi Hajja Kan ce suyi hakuri yarin ta ce, yaayinda shi Kuma Malam ke cewa Dan shi jarumi ne, w Haka ya tashi da zuciyar cewa shi he's superior to everyone he came across, ya Zama Wanda Babu Wanda zai iya tankwara shi se dai yayi abinda yayi niyya a lokacin da ya ga dama. Wannan shi yasa da suka zo tankwara shi se Suka kasa. A hankali ya dinga tuna rayuwar da yayi a wañnan gidan, kamar picture Haka suka dinga wucewa ta idanun shi, hannunshi ya dunkule in a fist kafin Kuma ya juya Dan he knows he looks pathetic bazai iya Shiga a Haka ba. Cikin sauri ya juya Dan barin gurin Amma se yaji wannan muryar me cike da dattako, dijantaka, hakuri da sanyi yace " Junaidu Ina zaka je Kuma?" A Haka ya tsaya Bai motsa ba sede dukkan jikin shi a sanyaye yake, har wani rawa yakeyi. Malam ya karaso tareda saka hannun shi ya ruko na Junaidun Wanda Yana juyowa ya rungume Malam din, ya saki ajiyar zuciya Malam ya Kashi Suka shiga ciki Kan shi a kasa kana kallo kasan a takure yake ga Kuma kunya me tsanani data lullube shi. AFIYYA is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258 [15/02, 23:10] +234 703 364 5886: 53 Babu kakkautawa alarm din da aka seta a wayar ya cigaba da ruri Wanda yasa Kara dunkukunewa cikin quilt din , ganin alarm din bazai kashe Kan shi ba yasa ta zuro hannunta Wanda yasha artificial nails an painting dinsu da white nail paint da wasu stones a jiki da a zahiri ita ya kawata ta Amma a gaskiya it looks dirty. Wayar ta janyo har lokacin bata fito da fuskar ta ba, tsaki ta buga tare da tashi ta zauna Wanda hakan yasa quilt din yin nashi guri Wanda ya bayyanata, she looks disheveled, gashinta dukka a barbaje kamar wata bishiya, fuskarta tasha Mai Dan kuwa ba se an fada maka bleaching take ba. Jikinta sanye da bum short da half vest. Wayar ta dauka tareda karawa a kunne Ashe bama alarm din bane Husna kawarta ce ke kiranta, tunda taga lokacin da ta Kira tasan definitely something is up, " Husna bacci nakeyi" Ta Dan yatsina fuska tace " Me zanyi a Whatsapp Kuma? Just tell me" Ta Dan Kara sakin tsaki tace " Ok Zan duba, I'll get back to you!" Daga Haka Nusaiba ta kashe wayar tare da sakko kafafunta ta zura cikin wani soft bedroom slippers, toilet ta Shiga ta wanke fuskarta tayi alwala tayi brushing, tana fitowa ta samu har an canja spread din gadon, sallayya ta shimfida ta hau Bayan ta saka jilbab Wanda ya rufe duka jikinta, agogo ta kalla har Tara saura, hakan yasa ta yatsina fuska ta tada sallar asubar da batayi ba akan lokaci. Seda ta idar ta dauki coffee din da aka aje Mata a gefe, ta juya tana ta hura hanci ta dauki tea spoon tana juyawa ta fara Sha a hankali sannan ta cewa me Mata gayran dakin ta Bata wayar, ta Miko Mata cikin ladabi, ta karba ta kunna data sannan ta jira komai yayi settling kafin ta duba message din Husna da ya shigo, tana dubawa taga pictures ne da yawa se videos Haka, ta shiga budawa tana jin ko menene tabbas Yana da muhimmanci da Husna zata Mata sharing. Yana Gama budewa da wannan video namu na swing ta fara cin Karo, idanun ta ta ware sosae tana kallo har ya Gama cikin sauri ta Kara kunnawa tana zooming fuskata, ganin bazai Yi ba ta bude sauran pictures din, wani Wanda Janet ta Mana a bakin mota ranar da ya raka ni tutorials school, tayi zooming tana kallon fuskata da wani farin ciki da yake a kwance bama ya bukatar se an fada. Aje login coffee din tayi ta bar wayar a gurin ta Shiga toilet, har ita Shehu zai ciwa mutunci? Yayi karya Bai Isa ba wallahi, wannan karya ne ta dinga ayyanawa bayan ta sakar ma kanta ruwa me dumi, cikin hanzari ta Gama wankan ta fito ta shirya a gaggauce cikin wando da riga ta daura jacket wadda iya karta kugunta, ta yafa wani firirin mayafi hade da saka takalmi wani high wedged sandals. Fitowa tayi rike da wayatta saboda yadda ranta ke bace Bata ma ga alamar Kiran da Husna tayi Mata ba. A parlor ta tadda wata dattijuwar mace, itama kana kallonta kasan Yar duniya ce, fuskarta is wrinkled Amma alamar shafe shafe Yana nan tattare da ita. " Mama zanje Law firm din Usman" Maman ta kalleta tace " Meye Kuma hadin ki da Usman? Ina ce maganar ku ta tashi" Ta girgiza Kai tace " Idan na dawo Zan Miki bayani, I need to go" Daga Haka ta finciki Jakarta tayi waje, maman tayi murmushi tace " Banda wauta ki samu miji kamar yaronnan lokaci daya ki juye kice ba Haka ba. Allah ya kyauta" Nusaiba na fita office din Shehu ta nufa, tun da ta Isa Secretariat shi tace Mata ai baya nan, kwana biyu Bai zo ba Yana hutu. Ko amsa Bata Bata ba ta juya tana fadin " Yau har gidan su zanje, ta Yaya zance na bar Abu sannan wani ya dauka, ai idan na bar Abu bazai cigaba ba sede ya lalace!" Lokacin da ta Isa kofar parlon, sarki na kokarin fitowa daga gidan, ya kalleta ya Kuma kalli kayan jikinta ya matsa ya Bata guri ba tareda ya Mata magana ba, he hates yarinyar to the square of infinity, ya ga wautar Shehu da ya kalleta yace Yana sonta, the girl is so artificial, komai nata jabu ne. He was so happy lokacin da ya fara ganin hankalin shehun ya fara rinjaya wajen Afiyya yasan definitely zai bar Nusaiba ya koma can, se kuma aka samu akasin wannan auren Amma dukda Haka yasan Dan uwanshi Bai hakura ba, yasan a zuciyar shi burin shi auren Afiyya ne. Ya ficewar shi Bai koma ba Dan yasan Ummiey will handle everything squarely, tana shiga ta samu Daddy da Ummiey na karyawa, tunda Ummiey ta amsa Mata sallama taji kamar ta koma, dama Basu taba haduwa da juna in person ba, sede kowa Yana da labarin kowa, Ummiey ta dubeta tace " Zauna Bari a Kira Miki Nadia" Ta girgiza Kai tace " Gurin Usman nazo" Ummiey tayi shiruu tana tunanin waye Kuma Usman se ta tuna Ashe ubanta ne Usman din, ta Kara kallonta kafin Kuma ta tura kujerar ta baya ta dawo parlon tana Kare Mata kallo, Daddy shidai Bai ce komai ba se abincin shi da yake ci Yana Kuma sauraron su, " How are you two related keda Usman Dina?" Nusaiba ta kalli Ummiey sannan ta Dan fara Wasa da hannunta ba tace komai ba " Bakiji ba? Meye tsakanin ku keda Shehu? I mean Usman" Ummiey ta Kara maimaita Mata, Nusaiba ta dubi Ummiey tace " Ni budurwar shi ce" Ummiey ta zaro idanun waje yayinda Daddy dake cin abinci ya kware, cikin sauri ya tsiyaya ruwa ya fara sha, Ummiey ta dubeshi sannn ta maida hankalin ta Kan Nusaiba tace " Are you Nusaiba? Kece?" Ta gyada Kai tana jin dama wannan ce uwar Shehu, ai ita Bata taba tsayawa gaban wani ba ta kasa yin abinda tayi niyya ba, sewannan matar ta kasa Koda kwakwarran motsi. Ummiey ta Kara kallonta tace " Look! Duk ranar da Kika koyi descent dressing you can come back here, wuce ki tafi!" Nusaiba kamar ta hantsila Haka ta fice ranta a mugun bace, Allah wadaran wannan matar, tana zuwa gate suka hadu da Nads da Harith. Nads ta tsaya suka gaisa sannan ta fada Mata Shehu na London, Nusaiba ta dinga rokon ta seda ta samu contact din shi na can kafin ta tafi tana jin abinda Ummiey ya Mata ba komai bane indai har ta samu contact din da zata sameshi ta ci Masa mutunci. Afiyya is not free pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258 [15/02, 23:10] +234 703 364 5886: 54 Tunda na sakko akan gado nake jin zuciyata Babu dadi, na dai daure nayi wanka Amma Ina Zama akan gado Dan fara shiri se na fara kuka, a hankali sautin kukan ke fita, inama inada dama na ayyana a raina da bazan Bari ya tafi ba, wannan satin biyun da yayi a tare damu ba karamin farin ciki ya saka ni a ciki ba, ya saka na tuna lokuta da dama na rayuwata ta baya, yasa ya Kara samun babban matsayi cikin zuciyata. Na share hawayena Ina murza Mai a jikina har lokacin ban daina kukan ba, how I wish he will stay with me and be my one, to Babu yadda zanyi Dole zai tafi Dan kuwa komai is not formalize. Na Kara goge fuskata Ina jin kamar na Hana shi tafiyar, na saka Kaya na wuce toilet na wanke fuskata sannan na fito parlor Amma dukda Haka Dana hango fuskata a jikin mirror se Naga idanuna sun danyi ja alamar kuka, na samu Nanny da Mom suna zaune, Nima na zauna Mom tace min da Bata lura da yanayi na ba " Yau Shirin ya dade, muje Kar yayi missing flight dinsa" Ba tareda na amsa ba na Mike tsaye da wayata a hannu na nufi kofa, se lokacin ta fahimci kuka nake yasa ta mike ta biyo bayana, " Menene abin kukan Kuma? Naga zaku dinga waya" Na gyada Mata Kai, tace " Jeki dakko shade ki saka sannan ki wanke fuskar ki, idan yaga kina kuka he'll be disturbed" Haka na koma nayi yadda tace sannan na fito shima lokacin ya shigo, clad in black trouser da Kuma turtled neck top me long sleeve ta ciki black ya daura suit a sama saboda har lokacin yanayin sanyin Bai Gama saki ba. Yayi kyau sosae na kalle shi Dan tunda na fito hankalin shi na kaina, ya karba key din motar hannun Mom muka fita bayan sunyi sallama da Nanny, na bi Bayan shi ni ya fara budewa seat din gefen shi na zauna ya rufe min sannan ya zagaya ya shiga ya zauna ya tada engine. Mom ta tuna Masa akan zamuje office din Dad suyi sallama Dan shi ba zai samu damar yin rakiyar ba. Tunda muka tafi motar shiru Babu me yin magana har mukai parking gaban katon building din, Yana kokarin fita Mom ta dakatar dashi da fadin " Zauna kawai Bari na same shi mu fito" Yayi murmushi Dan ya fahimci she's giving us some space muyi magana, tana fita ya dube ni all worried yace " Damsel! Me yake damunki?" Na girgiza kaina bayan na Dan bashi brief kallo he looks worried and disturbed. Na juyar da kaina jin hawayen na Kara taruwa a idanuna, ya saka hannun shi ya janyo fuskata tareda zare shades din Dana saka, ai tuni se hawaye ya balle min, na daura fuskata akan Bayan hannun shi Ina kuka a hankali, ya Dan saki siririn tsaki yace " Look Damsel ki daina kuka, Nima kaina I wish Zan iya Yun kukan saboda na nuna Miki zanyi kewar ki idan na tafi, but at least idan na tafi na barki kina kuka hankalina bazai kwanta ba Zan ta tuna yadda muka rabu" Na saki ajiyar zuciya Ina jin dukkan kalaman shi, na dago da jajayen idanuna da Kuma fuskata da tayi kacakaca da hawaye nace " I'm going to miss you terribly" Ya danyi murmushi me ciwo yace " It's same here, I promise you I'll be coming often zamu dinga magana kullum kinji? Know that Ina sonki, a gurina you're irreplaceable kinji?" Ya fada Yana sakar min tattausan murmushi tareda bani karamin yatsan shi Dan yaga Ina kallon shi irin Are you sure dinnan, ya gyada min Kan shi, na bashi yatsan nawa muka kulla yace " Deal sealed!" Nayi saurin sakin hannun saboda nasan abinda nayi ko nace mukai Babu kyau, na saki murmushi na maida hankalina Kan shi nace " To kaima kayi kukan Naga da gaske zakai missing Dina". Ya fara min dariya da tafa hannun shi yace " Idan maza sukai kuka ai Babu kanta, know that I'm gonna miss you" Na gyada kaina Ina Dan Kara jin Babu dadi. Mom ta karaso tare da Dad sukai sallama sosae Yana ta Masa godiyar zuwan da yayi. Daga Haka mukai sallama muka wuce airport shi Kuma ya koma ciki, mom Bata fito ba tayi Masa sallamar daga ciki sannan tayi.min alamar na bishi, tare muka dauki luggage din har zamuyi gaba tace mu tsaya tayi Mana hoto sannan Kuma muka wuce, seda aka Gama dukkan wasu formalities da Zan iya tsayawa tare dashi kafin Kuma yazo ya tsaya gabana yace " Zan tafi, I love you!" Na Dan Yi kasa da kaina Ina Kara jin ba Dadi nace " I love you too" Ya saki wani murmushi me taushi gaske so Charming nake fada muku yace " You finally said the L word!" Na rufe fuskata Ina dariya se Kuma wauan shi ta fara ringing, ya Dan Jima Yana kallon wayar kafin ya Kara kunnen sjhi Yana min alamar nayi excusing dinsa " Nusaiba?! Ina Kika samu contact Dina" Bansan ta ba Amma a family banji ance munada Nusaiba ba, hakan yasa a wayance na tattara dukkan hankalina Kan sauraron abinda yake fada, yeah sure I'm eavesdropping Amma ba zaka ce ba " Har ka Isa ma? Why will you be happy bayan nayi dumping dinka" " Dumping?!" Na maimaita a hankali Ina Kara faking looks Dina, yace " Nusaiba look, Dan mun taba relationship Bai Baki right ki.." " Ohhh! Har zancen right kake? Kalla abinda ka samo ka rasa me zaka so se wani Kashi da Rai, kaci min mutunci da zaka so ni sannan ka kalla wannan abar kace kana so. Thank God I dumped you" Abinnan ya min ciwo, ya kalleni Dan zargin ko naji Amma se yaga wayata nake dannawa yace " Don't drag her into this mess! Kuma na barki ne kije da pride din ki shiaysa ni ban fara dumping din ki ba, tun Muna tare na ganta..." " So you cheated on me? Da wannan guntun wanin, ai nayi tunanin zaka nemo wadda ta fini ne Dan naji haushi" Yayi dariya wadda tasa na kalle shi yace " Ni ba competition nake dake ba, sannan ki snai ita din tafi min ke say dubi, if I'll start over I wouldn't have dated you and ki sani I regretted dating you!" Yana Gama fada ya kashe wayar shi, nasan duk inda take se taji kamar ta mutu Dan takaicin abinda ya fada, ya kalleni lokacin aka fara announcement akan zasu fara Hawa jirgi Dole mukai sallama seda ya kulle sannan na juya na fito daga departure hall din. A hanya Mom tace min " Afiyya darling yake cewa Wai ko karshen shekara ayi muku aure, se nace ya Bari ki Gama makaranta" Billah unconsciously nace " Mom shekaran wajen uku fa, he'll be drained of waiting" Aikuwa ta fara dariya tana tsokana ta Wai dama so take taga reaction Dina, naji kunya sosae yadda Baku tunani. " So me kake so nayi yanzun? I gave you chance kayi Wasa dashi" Hasher ya Kara Bata fuska, why is she not understanding " Ammi ya kamata ki gane halin da nake ciki, how on Earth Zan Bari ta aura wani?" Anty Bintu ta Kara kallon shi tace " Hasher ka bar Afiyya tunda ta furta maka shi take so you please leave her, don't confuse her more" " Ammi Ina sonta!" " Shi ne dalilin da zaisa ka barta din, kasan abinda na yadda a soyayya, if you love someone is not necessarily making that person yours, you let him go as far as that person is happy it's ok! I know it's hard do it Hasher" Ya Jima shiru yana tunanin duk tsawon watannin da sukai me yasa Bai fada Mata Yana sonta ba se yanzun? Kai bazai Bari ba he definitely need to do something Kuma. Ganin yayi shiru Anty Bintu tace " Kai da Babana duk daya kuke, I'm so glad shi ne yake sonta ba bare ba, yarinyar nan has gone through alot Wanda ni a shekaruna ban dandani rabi ba, Hasher please ka kyaleta tayi farin ciki, don't stress her more' " Ammi kenan Baki Sona da ita?" Anty Bintu ta girgiza Kia tace " Ka fahimce ni Hasher, baka San Afiyya ba I introduce you to her and vice versa, naso kuyi aure Amma nasan Shehu ya kasance tare da ita tun kafin ta sanka ni bansan Yana sonta ba shiyasa nake baka hakuri! I'm sorry son" Ya gyada Kai bawai Dan ya hakura ba se Dan ya kwantar Mata da hankali! Afiyya is not free pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258. [15/02, 23:10] +234 703 364 5886: 55 Tamkar hasken Rana Haka gidan yake bakace wannan lokacin yayi Kama da Bayan sallar ishai ba, kowanne kwai ya haske gidan ya bada asalin kyau. Babu kowa a tsakar gidan se wata Mata da shekarunta zasu tasar ma ashirin da hudu zuwa biyar, tana sanye da maxi bubu Amma dukda Haka seda cikin jikin ta ya bayyana, tana tsaye da waya a kunnen ta alamar waya take, Jin sallamar Malam da Kuma Junaidu yasa tayi saurin juyowa, ta saki wayar ta Fadi Akan dabdanyar interlocks din da suka malale tsakar gidan. Ta nufi gurin fuskarta dauke da madaukakin annuri ta riko hannun Junaidu tace " Yaya Junaidu! Kaine? Kaine ka dawo gida?" A hankali Junaidu yace " Zainab kece Kika girma Haka?" Se ta juya cikin gidan tana fadin " Hajja! Baba!! Ummaah!! Anty!!! Ku fito Yaya Junaidu ya dawo" Ina tunanin hatta makwabta seda Suka jiyo maganarta, ta dawo ta rungume shi tana sakin kuka, karku manta zainab ita ce sanadin mafarin komai, dalilin ta aka fara takun saka da shi da Fatima har yayi sanadin fadawa abinda yake Yi. Hajja ta fara fitowa se Ummaah wato Fatima wadda kullum tana jin kamar ita ce dalilin lalacewar shi, ita ce sular barin gida shiyasa kullum cikin adduar ta tana roka Masa ranar da zai dawo gida ta samu ta rikeshi gafara shima ya roki gafarar iyayen shi. Hajja ta karasa ta rungume shi Dan tuni zainab ta sake shi ta matsa gefe, Hajja ta fshe da kuka tana ta shafa fuskar shi tana fadin " Allah nagode maka, Allah nagode da ka karba adduaya ka dawo min da yarona gida, Allah nagode maka" Ya rike hannayenta Yana jin wani irin abu a cikin zuciyar shi, ran shi da Kuma jikin shi, wani yanyai ne marar misaltuwa, wani irin rauni yake ji tamkae bashi dinnan bane Wanda no matter abinda ya faru zuciyar shi Bata motsawa, Amma kawai se yaji Abu Yana bin kuncin shi, ya saki hannun Hajja ya taba se kawai yaga hawaye ne, shikam bazai tuna last time da hawaye ya fita a idanunshi ba, me yasa yayi Haka? Ya dinga Jin Babu dadi,zuwa wani lokaci Yara duka sun fito kadan ya gane a ciki Amma sauran duka Bai tuna su ba ko ya tafi aka haife su ko Kuma suna Yara ya barsu, Amma cikin su kowa yasan shi saboda Babu ranar da zata zo ta Fadi baayi maganar shi ba, wasu da suka San gidan shi har zuwa suke wajen Afiyya wadda Basu San Bata nan ba. Parlon Hajja aka zazzauna aka kawo Masa abinci Wanda tun safe Bai Kara cin komai ba, komai ya canja hatta iyayen nashi sun Kara manyanta sun tsufa. A Daren jamilu da Anty Jidda Suka zo sauran ne ma suka Bari seda safe. Bai San dalili ba wanann Daren se yaji bacci yake cikeda nutsuwa Wanda wani lokacin se yayi ta munanan mafarki ko Kuma abinda yake son cikawa zuciyar shi Wanda gashi duk yadda ya kamata ace ya cika burin abin yaki yiwuwa. Washegari Malam da Junaidu da sauran yaran maza Suka tafi massallaci, tamkar mafarki dukkan su Haka suke ji to Amma Kuma waye yace Allah ba maji kukan bayinsa bane ba, ka roka ka daura yakinin cewa zai amsa maka tabbas zakaga biyan bukata, for 15years suna addua Basu gaji ba Basu yanke tsamannni zaa amsa musu ba se gashi Rana daya, minti daya Junaidu ya dawo gida, Junaidu yayi sallah wannan ai abin ayi murna ne. Da safe gidan ya cika se saukewa ake ana daurawa dukda kannen nashi na dardar dashi sanadin ko can ba sakar musu fuska yake ba, shi dinma wani iri yake ji musamman ganin yadda suke tsananin farin ciki da annaashuwa se Kiran abokan arziki suke suna fada musu ai Yaya Junaidu ya dawo. Se dare sanann ya samu Suka kebe shi da Hajja da Malam, Babu wani tone tone da akai the only abinda Malam ya tambaye shi shi ne Ina Amina? Junaidu yayi kasa da Kan shi ya fara fadawa Malam duk abinda ya faru har zuwa yadda akai suka rabu. " Dama niyyar ku daga Kai har kawun ta bamai kyau bace, shiyasa ba zaku ga daidai ba har se Kun nema yafiyar ta. Dan Haka gobe ka shirya muje sannan namiji baya cika seda aure. Ya kamata kayi aure" Shi gaba daya Junaidu ya manta da cewar Yana da Erectile dysfunction, hakan yasa yayi sunkui da Kai yace " Malam zaka iya ma kawunnan ta magana su yadda na maida ita" Hajja tace " Aminar?" Ya gyada Kai yace " Ita din haske ce a rayuwa ta, na cutar da ita na zalunce ta har abinci nake hanata Amma kullum taga Nayi wani Abu marar kyau to se ta yimin magana Koda Zan kashe ta ne. Dalilin ta na dawo hayyacina, na dawo Kan tafarkin musulinci. Na Kuma tabbatar zuciyata son ta take a lokacin da ya kamata ace na tausaya Mata na Kuma kula da ita, Malam Dan Allah kayi kokarin ganin ka dawo min da ita, ita din HASKEN RAYUWA TA CE" Malam ya jinjina Kai tabbas Afiyya ta taka muhimmiyar rawa wajen gyara Junaidu dukda magana ce kawai tayi Amma wani lokacin bamu sanin how powerful words are, shiyasa duk lokacin da zakai magana weigh the words, baka San idan sun fita me zasu janyo ba, they can break soul, deform a heart, kasan me zaka fada shi ne kawai! Yinin ranar Junaidu yayi shi cikin zulumi dan kuwa Malam ya nuna Masa bazai iya ba, shi kunyar yarinyar ma yake ji da Bai ma santa ba, how he wish abinda ya faru Bai faru ba da yayi farin ciki, ya nunawa Junaidu wannan yakin nashi ne ba Wanda zai Masa wannan fadan ba shi zaiyi wannan fadan. Yayi shiru a dakin shi Yana ayyana ko ya Afiyya zatayi shi Bai masan Bata kasar ba yasan dai zaa same ta a ringim. Yana zaune se rehearsing yadda zai Mata magana yake " AFIYYA kiyi hakuri ki yafe min! Ki bani wata dama mu Kara Zama inuwa daya" Se ya girgiza Kai yace line din is too plain and odd. Ya Kara yin shiru kafin Kuma ya Mike Yana zagaya dakin yace Yana zuwa zai zube akan gwiwar shi " Aminatou nasan ke din haske ce, Dan Allah ki dawo rayuwata Dan na gyara kurakurai na da nayi a baya" Se ya girgiza Kai yace wannan Kuma yayi extreme da yawa , can se ya fita zuwa wani katon shago yayi sayayya iri iri wadda yake da tabbacin zata burge ta sannan ya dawo gida. Washegari da wurwuri Hajja Baba da Malam, jamilu da Anty jidda, Ambaby da Kuma shi kan shi me gayya me aiki Junaidu. Yasha manyan Kaya ya kafa hula Kama kallon shi kaga lafiyayyen namiji managarci Amma abin baa fuska yake ba. Ambaby na sane tasan Afiyya Bata nan Amma dai so take taga iya gudun ruwan kowa. Misalin Sha daya na safe suka Isa cikin garin Ringim, tiryan tiryan komai ke dawo Masa tundaga ranar da suka fara zuwa gurin ta yaki Mata magana zuwa auren su inda akai controversy akan sakin ta, ya nuna musu kankanci ta hanyar daukar ta cilak ya saka a mota ya tafi da ita, se yaji zufa ta karyo Masa ta Ina zai fara kuma,? Ta Yaya zai fuskanci Yan uwanta iyayen ta da ya batawa Rai a wañnan rana. Se yaji kamar yace su juya ya fasa but it's today or never! Se Kuma yayi tunanin ai inda ake Hawa to ta nan ake sauka Dan haka se ya kwatanta musu gidan Kawu Sa'idu. Suna Isa kofar gidan Yana fitowa daga ciki Allah basshi zakuyi tunanin shi din mahaukaci me saboda yadda ya fito a firgice tamkar Wanda Zaki ya biyo shi. Ya tsaya se waige waige yake kafin Kuma ya daga kafafun shi Dan tafiya motocin su Junaidu suka tsaya, Dole ya tsaya Dan duk tunanin shi Kawu Tijjani ne da yace masa zai zo Ringim din ranar, suna hada idanu da Junaidu yayi azamar komawa ciki se Malam ya dakatar dashi da fadin " Malam barka da safe!" Kawu ya tsaya Yana Dan haki yace " Barka dai! Me ya kawo ka kofar gidana ko kazo ka karasa ni ne da Raina?" Malam ya danyi gyaran muryar yace " Allah ya huci zuciyar ka ni din mahaifin shi ne, nazo muyi magana ne" Kawu ya dallawa Junaidu harara sannan Kuma ya Shiga ciki se gashi ya fito da tabarma, matan yace su shiga ciki, tunda Ambaby ta Shiga da Jidda suke Willa idon ganin Afiyya Amma shiru har Siyama ta baza musu tabarma wadda auren nata yake lilo shi Bai mutu ba shi Kuma baa zauna ba. Suka zauna suna zazzare idanu, ta debo musu a katon Kofi ta aje sannan ta koma daki ta zauna, Ummaan su ta fito Wanda da batayi niyyar hakan ba, Suka gaisa tace " Daga Ina hakan ban gane ki ba" Hajja da fara'ar ta tace " Iyayen tsohon mijin Amina ne" Ummaah ta kalle su tace " Wacce Aminar kenan? Ni Amina ta iyayen mijinta daya, tana gidan mijin ta" Se lokacin Ambaby tace " Anty Afiyya muke nufi" Wani mummunan kallo ta fara musu tace " Nan yayi muku Kama da gidan su Afiyya ne ko meye, malamai ku fitar Mana a gida" Ta fada tana Jan tabarmar kamar zata jirkice su, Siyama dama na tsaye tacw " Haba Ummaah..." Kallon da tayi Mata yasa tayi saurin rufe Baki, tuni sun mike Siyama tace " Ai Afiyya batayi sati biyu ba a garinnan ta tafi London, inaga sede kuje kano gidan Kawu Tijjani" Su Ina Suka San wani Kawu Tijjani, Haka Suka fice ransu a bace suna iya jiyo muryar Ummaah na zazzagawa Siyama fadan ta kulasu itama ta bisu tunda nan ba gidan aurenta bane, ita kuwa tayi shigewar ta daki ta Mata kunnen uwar Shehu! A kofar gida hakan ce ta faru Dan Kawu Sa'idu kamar zai daki Junaidu ya nuna Masa shi ne silar lalacewar komai, munafurci ya dawo dashi. Wannan kenan A bangare na, na dawo gida washegari na fara exams sede dukkan wani Abu da nakeyi Ina tunani shi ki nakeyi kamar nayi tsuntsuwa naje gare shi, har na gaji da tambayar Nads ko ya karaso, sede tayi dariya tace ita kuwa taha ta kanta. Na fito daga paper Primary health care se ga Kiran shi ya shigo cikin sassanyar murya nace " Honey!" Yayi murmushi Wanda naji sautin shi yace " Damsel kinata jirana ko? I'm sorry se yanzun na karaso ko gida ban karasa ba" Naji wani irin farin ciki ya lullubeni so I'm that important na tambayi kaina, yace " Are you there?" Na saki ajiyar zuciya nace " Ina jinaka ka karasa gida ka huta zamuyi magana. Allah ya huce gajiya my regards to everyone at home" Daga mukai sallama na wuce gida, bamu Kara waya ba se dare har nazo Zan kwanta, mun Sha Hira se can nace Masa " Honey waye Nusaiba?" " Hello!" Ya fada Wai ni zai nunawa Bai jiba, nace " I know you heard so I'm not repeating myself my Dear!" " Were you eavesdropping?" Na saki ajiyar zuciya Ina murmushi kadan nace " Mhmmm...Yes!" Yayi dariya ya fara min bayanin ta da komai sannan yace " Kinsan ke nake so ko? Please ki cire sunanta a ranki" Nace " Anya zan iya? Why did she call you then?" Ya Kara min bayani sannan nace " I was very mad at you! Daga yau don't talk to her again" " I promise you!!" Ya fada immediately sannan na Masa sallama dukda yaso mu cigaba da magana Amma na nuna haushin shi nakeji. AFIYYA is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258. [15/02, 23:10] +234 703 364 5886: 56 Duk wani abu da ake Babu abinda muka san Yana faruwa, rayuwar mu kawai muke not knowing it's a mess down there in Nigeria. Bayan anyi Babu dadi tsakanin Kawu Sa'idu da su Junaidu duk dasu Basu kulashi ba, Dole suka juya zuwa kazaure. Junaidu was more than depressed bayan komawar su gida. Kamar wanda zaiyi karamin hauka Haka yakeji. Ranar Yana zaune gaban Hajja da carbi a hannun shi ya dawo daga dakin Malam Wanda ya daura Masa karatu kamar yadda suke dukkan Rana. Yanzun ya tasar ma watanni uku da dawowa Kan track dinsa. Ya rame yayi Baki, gashin Baki da baya Tarawa da yake askewa yanzun duk sun fito saboda bama shi da nutsuwar zuwa wajen askin. Ta dubeshi tace " Yarona kaga yadda kake komawa kuwa? Ba zaka sanyawa zuciyar ka salama ba" Ya aje carbin idanun shi sun Kara kadawa sunyi ja, tamkar ba wannan Junaidun da kowa ya sani ba, gaba daya wannan ya sususuce ya Zama wani iri, a hakan Wai sallah na dawo Masa da nutsuwar shi. yace " Hajja zanso wani yaji yadda nakeji, kilan da kunmin uzuri, Ina jin zuciyata tayi min nauyi duk abinda nake tunanin ta nake, bana bacci me dadi se Ina ganin lokacin da nake dukanta nake azabtar da ita gashi yanzun Bata nan balle na nema yafiyar ta na Mata tayin soyayya ta!" Hajja cikeda tausayin Dan nata ta Raya Allah ke sakawa Afiyya ta hanyar darsa Masa sonta cikin zuciyar shi, ta sauke ajiyar zuciya tace " Babu Kuma Wanda ka sani nata? Amma ance tanada Kawu a Kano ko?" Se lokacin ya tuna tabbas tana da Kawu a Kano shi ne Wanda Kawu Sa'idu ke yawan cewa dolo ne da ace shi ke da dukiyar Afiyya da tuni an Gama zancen Amma da yake hannun Uncle Babawo take shiyasa suka kasa banbara. Cikin sauri ya fara tuanain yadda zaiyi ya samu address din Kawu Tijjani Bai kuwa wani Sha wahala ba ya samu. Washegari suka nufi Kano bayan Hajja ta saka jamilu ya raka shi yayi aski, ta sashi a gaba ya shirya ya Dan dawo hayyacin shi sannan Suka tasarma gidan Kawu Tijjani. Lokacin da Suka Isa ya fito Dan rakiyar bako, da yake bashida zafi ko kadan yasa ya tarbe su har cikin parlor ga Kuma daraja da kimar Malam da ya gani. Bayan sun gaisa an jajanta abubuwa se Kuma Malam ya fada Masa abinda ya kawo su. Kawu Tijjani ya kalli Junaidu Wanda yayi kasa da kanshi sosae mamaki ya Kama shi lallai Allah shi ke shiryawa gashi nan shekara da wasu watanni ko Kai waye baka Isa Junaidu ya sauke Kan Shi ba Dan Kuna magana sede ya zuba idanun shi cikin naka Amma abin mamaki yanzun shi ne yake kasa da Kai alamar Jin nauyi. " Ni da kake gani banida ikon yanke hukunci akan Afiyya, Babawo shi ne babanta shi muka bawa dukkan dama a kanta, balle Afiyya yanzun ko zatayi Aure musulinci ya Bata damar zabar mijinta da kanta tunda ba auren farko bane. Ina saka ran zasu dawo karshen wani watan se kayi kokarin daidaita kanka kaje ka Nemo yafiyar ta, zancen aurenta Wanda kukaga ya fita yanzun shi ma Neman aurenta yazo Dan Haka lissafi ya rage naka" Ko Babu komai maganar da Kawu ya Masa cikin tattausan lafazi yasa ya danji hankalin shi ya kwanta sede Kuma ya fara jin tsoro saboda yasan indai Afiyya ce zata zabi mijin ta ba zata taba zaben shi ba Haka wannan kawun nata me masifar bin diddigi, dama Yana ta adduar ba hannun shi take ba Amma adduar shi Bata ci ba. Na Gama exams har munyi hutun sati uku Wanda sati biyu a NY nayi shi, naje na tarar Rooks tayi kiba ta Zama babbar mace kamar Amina Abubakar Rogo, ni ce dai Yar firit a cikin su. Wannan sati biyun da nayi na Yi shi cikin farin ciki da Jin Dadi, na dawo gida Dan daura sabuwar semester. Tsakanina da Yaya Shehu soyayya me karfi kullum ke Kara shiga tsakanin mu, shi din aboki nane, shi din masoyi name Wanda nake jin son shi a dukkan sassan jikina, wani lokacin na Kan auna wani Abu ya raba ni dashi nakan ji hankali na ya tashi iya ayyanawa da nayi. Shi din Rabin jikina ne Wanda na samu solace a tare dashi. Shi din wani bangare ne na rayuwa ta Wanda bazan iya ba se dashi,ban taba jin son Abu kamar yadda nake son shi ba, how I wish Abbuna da Mama ta suna raye suga namiji guda daya ya tsaya min a rayuwa. Ni dashi cikin aminci muke soyayya min riga min fahimci junan mu so deep,nakan Yi mamakin a lokaci kankani yadda ya fahimce ni Nima na fahimce shi har Haka. No matter what, duk abinda ya faru zamuyi magana Koda chat ne bana tunanin akwai watarana da tazo ta tsallake bamui magana dashi ba Wanda ya assassa Kara shakuwar mu dashi. Bangarena da Yaya Hasher ya daina kulani wani lokacin na Kan duba last seen dinsa and idan Naga Yana online Bai kulani ba se naji Babu dadi, ko Babu komai ya nuna min kulawa lokacin da nake bukatar hakan, wani lokacin se na aje pride Dina na Masa magana but yadda yake replying Dina ke Bata min rai se na tattara shi na watsar dashi Nima, I know ni ban yaudare shi why will I be accounting for zargin da yake min. Wani yammaci min kammalla abincin dare na dawo daki Dan returning call din Yaya Shehu, ya kirani nayi picking nace Masa Zan Kira shi I was a bit busy ne. Dakin nawa wajen study table Dina duka a hargitse saboda exams da nake, karatu nake ba na Wasa ba. Na zauna na fara Kiran shi se ya kashe ya kirani yace na kunna data muyi video call . Na kalla kaina I was clad in skirt da riga na atamfa, ta wajen hips din ya kamani soosae Wanda ya tabbatar min na fara kiba Nima, Amma saboda yadda nake son kayan yasa naki cirewa, veil nayi draping saman kafadata ya lullube duk inda ya kamata sannan na kunna data Wanda immediately Kiran shi ya shigo, Yana zaune a office he looks tired, nayi murmushi nace " Somebody is tired!" Ya shafa Kan shi yace " Extremely Baby! Ya exams din?' Na haska Masa study table Dina Ina jin shi Yana dariya kafin na dawo da wayar inda nake, muka Dan taba Hira se na Mike na fara tattara books din, se kawai naji yace " Mashaaa Allah! Damsel kiba kikeyi, kin sani?" Nayi saurin Jan veil din Dan ya rufe min hips dina Ina pouting se yayi dariya tareda lumshe idanu yace " I'm sorry zamuyi magana da daddare ko?" Na gyada kaina har lokacin kunyar yaga abinda nake ta boyewa nake shi Kuma ya Mike ya tattare kayan shi ya tafi. Muna zaune muna cin abinci wayata Dake cikin pocket Dina ta fara ringing, nayi saurin hadiyewa na Ciro wayar se Naga Kawu Tijjani ne, na Kora apple juice din dake cikin tumbler sannan na Kara wayar a kunnena cikeda farin ciki yace " Daughter ta" "Abiey! Ina Basma" " She's here, Ina Dad dinki?" Na kalla Dad da ya meda hankalin shi Kan broccoli salad din da yake ci nace " He's here" Se da muka gaisa yace na bawa Dad ya kira shi Bai sameshi ba, na Mika Masa wayar Ina fada Masa Kawu Tijjani ne. " Man! Wallahi wayar na daki I'm having dinner ne" " You want to talk to me! Ok..." Daga Haka ya Mike ya nufi bedroom dinsu ni Kuma na maida hankalina wajen cin abinci. AFIYYA is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258.57 Har muka gama cin abinci Babu alamar fitowar Dad, ni Kuma naki tafiya saboda I was waiting for my phone, na tabbatar Honey will call. Nayi shiru Ina kallon TV Amma ko kadan bani comprehending abinda ake Yi balle abinda ake fada. Itakam da Nanny Banda hirar su Babu abinda suke yi, can na Mike na nufi daki na dakko system dinta Dan washegari inada mental health exams da Rana, na saka slides din a gabana na kura idanu, yawancin ban Faye son course din ba especially Schiz dinnan dukda Yana da sauki Amma wannan positive and negative symptoms ke Dan confusing dina, mum ta dubeni Lokacin I was going through OCD tace " Karar TV Bai damun ki ne? Ki tafi daki indai karatu kike so kiyi" Na Dan Yi pouting nace " Wayana a gurin Dad" Nanny tace " Nayi mamakin abinda ya zaunar dake Ashe shalele ce hannun Alhaji" Duk lokacin da tace Alhaji se Abbu ya fado min , na murza hannuna a idanuna Ina fadin Allah ya jikanka Abbuna I so much missed you! Mum ta mike Babu jimawa se gata da wayata ta Mika min na amsa da sauri tareda duba call log dina, na saki ajiyar zuciya ganin Bai Kira ba, na tattara system Dina na wuce dakina. Ban Dade Ina karatu ba bacci yayi gaba Dani. Washegari I woke up to calls dinsa da nayi missing, Ina kuwa idar da sallah na Kira shi Bai dauka ba se kawai na cigaba da sabgar gabana. Na fito na samu Babu kowa a parlon se na wuce kitchen Dan duk tuanani na Basu tashi ba, Ina shiga kitchen na hada tea na fara Sha sannan na fara hada brown yam da tuna sauce, ba jimawa na Gama na fito se Naga Nanny, Mom da Dad sun fito a tare daga dakin Nanny, Mom fuskarta ta nuna alamar tashin hankali Dake ita Haka take Bata iya boye damuwa a tattare da ita, Nanny Kuma tana kallona with my sympathy a idanunta. I was like irin eh! Meye Haka? What are these people doing together this early morning? Na cigaba da kallon su har suka karaso parlon kafin na Dan tattaro courage na gaishe su Dad ya fara amsawa sannan sauran biyun. Na juya na hado komai na karyawa sannan na dawo parlon. Mum na min murmushi ni Kam duk jikina yayi sanyi, what's happening? Dole akwai wani Abu da zaisa da sassafe su kafa meeting kamar wasu UN. Na dai zauna Ina yake Dad ya dubeni yace " When are you writing your last exams for this semester?' Na aje cup din hannuna nace " Yau ne!" Ya gyada Kai tareda fadin " Se ku Zama cikin shiri we will be flying back to Nigeria cikin satinnan. Ai hutun ki da yawa ko?" Na gyada Kai tareda bawa Mom questioning look se ta dauke kanta daga kallona ta mayar Kan abinci, a take naji abincin ya fita daga raina, naji ko kadan bazan iya cin komai ba, na karasa shanye tea Dina lokacin takwas da rabi na wuce daki nayi wanka se school Kuma har lokacin shima Bai kirani ba. Na jima da wayar a hannuna Ina tunanin what kept him this long baiyi returning call ba se gashi ya kira, na Dan Bata fuska kamar Yana gabana sannan na dauka nace " Nayi fushi" " I'm sorry Damsel! Was a bit busy. How have you been?" Na Dan yatsina fuska Dan na haddace wannan gaisuwar tamu nace " I'm fine alhamdulillah! Na Gama exams!" Yayi Dan karamin squealing na Taya ni murna sannan yayi min addu'oin nasara yace na tafi gida idan na Isa na kirashi zamuyi magana. Hakan kuwa nayi Ina kashewa nayi sallama dasu Janet da Maryam na nufi gida, dukda sun so muyi pictures naki nace musu sauri nakeyi. Ina Isa gida tun a Hanya na hanga Nanny tana Shiga gida, ta fita strolling na ayyana a raina, bayan na shiga gida na tarar Babu kowa a parlon, mamaki ya Kama ni ganin ko minti biyu cikakke baiyi da Naga shigarta gida, na cire veil din na Yar Kan sofa sannan na bishi na danne tareda lumshe idanuna Ina jin wani ease a jikina, se kawai naji muryar Mom na fadin " Surprise Afiyya!" Nayi saurin bude idanuna a take na hango cake anyi frosting dinsa, yayi kyau Ina tunanin 8 inches cake ne. Nayi saurin mikewa bakina wide into a wide grin nace " Mom" Ta shafa kaina tare da fadin " Happy birthday! I wish all the beauties of life!" Na rungume ta Bayan ta aje cake din se lokacin na lura da pastries din da aka jera a dining, har Raina na manta da wani birthday dina yau, na sauke ajiyar zuciya na wuce daki bisa umarnin na canja Kaya. Nan na samu gift Akan gado, na Dan daddaga Amma Kuma ban bude ba nayi changing zuwa wata flowing gown da tayi min kyau, na hada kaina in a ponytail sannan na dakko hair band na saka kalar gown din tareda makala 10 inches pointed high heels. Powder na shafa hade da khol sannan na feshe jikina da turare na fito, Nanny ta fara rungume ni, tareda riko hannuna tace " Kamar yau ne aka haifeki, na tuna an aiko Mana Lagos cewar Waziri baya da lafiya shi ne abinda yasa mamanki ta Shiga labor da baa shirya ba. Gashi yau har kin cika Sha bakwai! Allah ya raya ki" N rungume ta Ina Dan goge hawayen dake barazanar Bata min fuska nace " Nagode sosae Nanny, nagode da Kika tsaya cikin rayuwata! Allah ya jikan Mama da Abbu" Ta sharen hawayena tareda fada min nayi farin ciki. I was so happy da Ina yanka cake din, Mum tasa maid dinmu tayi videos da hotuna, can Naga Mom taje amsa call ba jimawa ta dawo tace na saka dankwali akaina zatayi Baki, Haka na saka karamin veil na yafa a take na Kara yin kyau, ga mamakina se kawai Jin sallamar Honey nayi, na Mike daga zaunen da nake cikin sauri na nufe ahi, kunsan Allah Banda ya kauce wallahi da rungume shi zanyi, baa taba min surprise me dadi irin wannan ba, na kalleshi yayi kyau cikin maroon din long sleeve top Amma Kuma ya nade hannun sama se Kuma wandon pale blue ne. Yayi kyau da wannan Charming smile din nashi, na tsaya se Kuma na Bata Rai na juya Ina kallon Mom Dake kallona with so much amusement a idanunta nasan tana weighing kaunar da mukewa juna ne. Na tsaya gefen ta Ina tura Baki nace " Kinsan yazo ko?" Tayi dariya tace " He wanted surprising you!" A waje inda wasu wooden chairs suke muka zauna, se kallona yake Yana murmushi yayinda na hade fuska Amma Kuma cikin zuciyata ji nake kamar nayi ihu na Kuma Yi rawa. He told me tun jiya ya taho Dan kawai ya kasance Dani a Rana ta Mai muhimmanci, ban ma Kara fushin ba na hakura da yamma muka fita yawo na manta da duk wata damuwa da matsala, shi kadai nake gani a duniya, Kai duniyar ma ji nake kamar daga ni se shi muka rage. Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 0906346725858 Bamu dawo gida ba se yamma Dan Muna shigowa ko Zama bamuyi ba aka fara Kiran sallah, na wuce daki nayi alwala nai sallah na zauna bare gift dina, na Dad da Mom da Nanny se Kuma nashi, kowanne content din yayi min kyau ba ma kamar nashi. Na Adana komai sannan na fito Jin Nanny na Kirana, na rungume ta Ina Mata adduar kyautar da tayi min, tace Mom Dina ke Kirana. Tana Kitchen na sameta tayi packaging slice cake da sauran finger foods tace na dauka na kaiwa su Sheriffa tunda ban gayyace su ba, Haka na dauka na fita anan inda muka zauna dazun na ganshi shi da Dad in a serious conversation kamar yadda fuskokin su ya nuna, na hadiye yawu Dan kawai jikina na bani something is fishy, akwai Dole abinda yake faruwa a Nigeria, ban wani maida hankali ba na fadawa Dad inda zanje sannan na wuce, ban Jima ba na dawo dukda Sheriffa kamar zata yanka ni saboda ban fada Mata ba, nace Mata Nima na manta gaba daya da hakan. Ina dawowa mukai dinner sannan na zauna kujeran Dake kallon wadda yake zaune yace " 2am ne flight dina" Confusingly nace " Zuwa Ina kenan?" Yace " Nigeria, Dad yace min jibi zaku taho ko?" Na gyada Kai trying hard Kar na nuna na damu so kawai muka Shiga hira yau da gobe Bai ce min komai ba balle Kuma ni da bansan ma abinda ke faruwa ba. A Daren ya wuce airport banma rakashi ba saboda na gaji ga bacci se kawai na kwanta Bayan munyi sallama. Washegari ya kasance duk hada Kaya ne, ranar Monday da sassafe karfe shida jirgin mu ya tashi zuwa Malaysia Dan se mun fara trans in acan kafin Kuma mu wuce gida wato Nigeria. Abinda yafi min dadi a wañnan tafiyar kasancewar dukka zamu hadu acan su Rooks ma sun riga da sun wuce. Agogon hannun shi ya kalla sannan Kuma ya samu guri ya zauna gefen Ummiey wadda ke kallon duk wani Abu da yake Yi, daga ita se shi a gidan Dan Nads da Harith sun tafi gidan su Rooks sarki da Daddy Kuma suna fada. Ummiey ta dube shi tace " Yaushe ne saukar su Afiyya din? Na zata zakaje Kano taho dasu" Yayi dariya yace " Ai Kawu Tijjani zai dakko su shiyasa" Ta gyada Kai tace " So da kaje Lancaster kayi Mata magana akan Hasher dinne?" Ya girgiza Kai yace " Ni ban Mata ba, bana son taji maganar a bakina Amma munyi magana da Mummy da Kuma Uncle Babawo yace min wai wannan tsohon mijin nata shima yazo Wai da family dinsa..." Da sauri Ummiey tace " Wai Junaidu? Amma ma dai a gaida Tijjani me karfin zuciya shi wannan yaron har ya Isa ayi Masa second glance." With lot of humor a muryar Shehu yace " Ummiey ni nasan afiyy ba zata taba zabar wani miji Bayan ni ba, so shiyasa banma bi takan maganar ba shi Kuma Hasher yayi contacting Dina akan maganar nace Masa ni bazan Yi fada da kowa akan ta ba nasan idan har ita zata zaba mijin ta Bata da wani se ni se Kuma idan Allah ne Bai nufa ba" Ta Dan bugi kafadar shi kadan tare da gyada Masa Kai tace " You have so much faith in her" Yayi murmushi Yace " I believe in her Ummiey" Ta musu adduoi sannan ya wuce daki Dan ya huta kafin karasowar su Afiyya. Karfe Tara na dare muka shigo garin Ringim, tun daga gate din legal nake ta kalle kalle ko Ina se Ina tuna memory that's lingered a wañnan gurin, har seda muka shigo cikin gari mukai parking kofar gidan da yake mallakin na uncle Babawo ne. Shekara biyu kenan da na bar garinnan gashi na Kara dawowa, sede I'm no more that naive girl wannan din wata sabuwar yarinya ce wadda ta Kara fahimtar rayuwa da Kuma zaman duniya. Muka fito zuwa ciki a matukar gajiye, Ina shiga nayi daki na fada Kan gado ko veil Dina ban cire ba, nayi shiru Ina lumshe idanuna a take kuwa bacci yayi gaba dani, nasan Ina baccin naji shigowar Mom da Nanny Amma banji fitar su ba, se Sha biyu sannan na farka idanuna har lokacin akwai bacci, na tashi na gyara kwanciyata na cigaba da bacci. Washegari da wurwuri mukai gyaran gida komai ya koma muhallin shi sannan nayi wanka naci abinci na koma daki ko wayata ban nema ba na sake komawa bacci. Wajen daya na farka nayi sallah sannan na fito parlor nayi kicibis da Nads da Rooks, suka yo kaina kamar zasu kayar Dani na fara musu ihun su sake ni Zan Fadi kafin Kuma na zauna " Mom dinki ta fita tun dazun kema tashi zakiyi mu tafi" Nace " Ina zamuje?" Nads race " Gidan Ummiey mana!" " Ummiey fa? A'a wallahi bazan je ba" "Kunyar surukai!" Na wuce daki na canja Kaya sannan na fito muka fita, iska na kadawa a hankali muka nufi gidan Mummy kamar yadda nace musu sede da mukaje Bata gidan, na Ciro wayata na saka Sim Dina na Nigeria sannan muka fara Hira se tsokana ta suke Wai jikin su na Basu kafin a Gama hutunnan zaayi min aure. Nayi dariya nace " Da an rage min wahala wallahi dama so nake na kasance da Honey kullum" . Rooks bakin ta kamar zai yage Dan mamaki yayinda Nads ke fadin " Lallai in law kice a matse kike" Na Harare ta " Ke Nads I'm your elder sister yanzun stop teasing me" Kafin ta bani amsa wayatta tayi ringing ta dauka Babu jimawa ta dubeni tace " Dad dinki na Neman ki acan gidan Waziri" Nace " Toooo!" Na mike Ina musu kashedin su jirani na dawo sannan su sayo Mana Dan malili muci idan na dawo se suka ce kawai idan na Gama na same su a gidan mu can zasu koma. A hankali na cigaba da tafiya har nazo kofar gidan Kawu Sa'idu, na tsaya ba tareda na shiga ba Amma se kallon zauren gidan nake rayuwa kenan. Komai ya wuce se tashin labari,na tuna lokacin da nake ganin rayuwa ba zata taba komawa daidai ba, na tuna lokacin da nake ganin Babu wani Jin Dadi a rayuwa , lokacin da nayi giving up akan rayuwar ma Baki daya lokacin gani nake banida wani hope na kara samun yancin but Allah ya nunamin shike da iko bani ba. Na juya na cigaba da tafiya nayi niyya Zan Shiga Amma ba yanzun ba se na dawo daga Kiran Dad. Na danyi nisa kadan naji muryar Hafsisi tana kwala min Kira, a sukwane na juya ita din ce kuwan da Sahib a hannun ta yaron Siyama, na saki murmushi lokacin da ta karaso tana fadin " Afiyya kin ganki kuwa?" Nace " Me nayi?" Tace " Innanlillahi se wani haskawa kike kin Kara kyau" Nayi dariya nace taje gida zanzo yanzun jirana ake, ta ruko hannuna tana tambayata kp da gaske zanzo nace Mata ai alkawari nayi.sannan na samu ta tafi ni Kuma na hanzarta naje. Shima gidan an gyara shi sede Ina iya hango guraren da mukai wasan kasa, guje gujen da komai, Allah sarki Hajiya kakata. Kofar parlon takalma me sunfi biyar hakan yasa gabana faduwa Amma na daure bakina dauke da sallama kaina Kuma a kasa na shiga, Mummy ta fara fadin " Mashaaa Allah Afiy xo nan" Na saki murmushi na Isa gareta tare da rungumar ta nace " Mummy Ashe kina nan? Ina wuni?" Ta amsa sannan na gaida Dad da Kawu Tijjani, Ina daga kaina Naga Kawu Sa'idu a zaune ya zuba min idanun shi, nayi saurin janye nawa na gaishe shi a ciki ciki kafin Kuma na Kai idanuna kan sauran occupant din, subhannallah! Kadan ne zuciayata Bata fito ba ganin Junaidu wani dattijo da Kuma wasu su biyu da ban San su ba. Gaban ya Fadi na dubi Mummy se Naga ta min alamar na gaishe su, bakina na Dan rawa na gaishe su, dattijon yace " Amina kece?" Na Dan gyada kaina kadan sannan Kuma na sunkuyar da kaina. Kawu Sa'idu Dake gefe yace " Tunda tazo se mu Basu guri Dan su sasanta kansu ko?" Da mamaki na dago cikin sauri na kalla Kawu Sa'idu, na kalla Junaidu da yaki dauke idanun shi daga kaina, se lokacin na lura da sauyi a tattare dashi, Naga wata irin nutsuwa da ban taba gami a tare dashi ba Amma duk ba wannan ba meye Kawu Sa'idu ke fada Haka? Ni da way zamu sasanta? Haba ba dai Junaidu ba wannan mafarki ne ma, mummunan gaske ma kuwa. Dad ya dubi Kawu Sa'idu yace " Ban zo gurinnan Dan na hada aure ba, nazo na bawa yata kariya ne, ni ne ubanta ni ne me hakkin zaba Mata abinda nake ganin ya dace da ita. Junaidu kace kana son ganin Afiyya gata Ina sauraronka" Naji dadin maganganun shi, naji karfin gwiwa da Kuma Jin Dadi a raina. Junaidu ya taso yazo ya tsugunna har gabana inda nake zaune ya dira gwiwar shi biyu a kasa sannan ya fara roko na na yafe masa, yasan ya cutar dani...bla..bla...bla... Tunda ya fara magana nake kallon shi, he seems moody, dukda dama bantaba ganin faraar shi ba Amma nasan da gaske shi din se a hankali, but yanzun akwai sabon Abu a tattare dashi. Kaina na girgiza nace " Duk abinda ka min, son ranka ne ban maka komai ba, Amma kayi min komai, Dan Haka yafe maka bakai zaka ce ba ni ce Zan gani idan ka cancanci hakan." Kowa yayi tsit nasan mamaki suke, Kawu Sa'idu ya fara kokarin magana Dad ya dakatar dashi " Right dinta ne idan taga zata yafe to? Ni bazan matsa Mata ba saboda ita kadai tasan wahalar da Tasha" Kawu Tijjani ya gyada Kai yayinda na dubi Junaidu he looks disturbed abin tausayi kawai Baki daya, da idanu na pleading I'm sure da su zaiyi amfani wajen plead din, na dauke kaina se naji muryar Dad na fadin " Ni fa na Gama magana ba zata koma gidan shi ba" Malam da se lokacin yayi magana yace "Aji ta bakinta tukunna" Dad yayi dariya yace " Afiyya Zaki koma gidan Junaidu?" Kafin ya karasa na girgiza kaina na Kuma bude Baki nace a'a Dole Haka Suka tashi Sika tafi sannan Dad yace min Hasher yazo musu da batun Yana sona, Yana son na nutsu sub bani kwana biyu na zaba ko Hasher ko Shehu, banma motsa ba kaina a kasa nace " Yaya Shehu na zaba!"58 Bamu dawo gida ba se yamma Dan Muna shigowa ko Zama bamuyi ba aka fara Kiran sallah, na wuce daki nayi alwala nai sallah na zauna bare gift dina, na Dad da Mom da Nanny se Kuma nashi, kowanne content din yayi min kyau ba ma kamar nashi. Na Adana komai sannan na fito Jin Nanny na Kirana, na rungume ta Ina Mata adduar kyautar da tayi min, tace Mom Dina ke Kirana. Tana Kitchen na sameta tayi packaging slice cake da sauran finger foods tace na dauka na kaiwa su Sheriffa tunda ban gayyace su ba, Haka na dauka na fita anan inda muka zauna dazun na ganshi shi da Dad in a serious conversation kamar yadda fuskokin su ya nuna, na hadiye yawu Dan kawai jikina na bani something is fishy, akwai Dole abinda yake faruwa a Nigeria, ban wani maida hankali ba na fadawa Dad inda zanje sannan na wuce, ban Jima ba na dawo dukda Sheriffa kamar zata yanka ni saboda ban fada Mata ba, nace Mata Nima na manta gaba daya da hakan. Ina dawowa mukai dinner sannan na zauna kujeran Dake kallon wadda yake zaune yace " 2am ne flight dina" Confusingly nace " Zuwa Ina kenan?" Yace " Nigeria, Dad yace min jibi zaku taho ko?" Na gyada Kai trying hard Kar na nuna na damu so kawai muka Shiga hira yau da gobe Bai ce min komai ba balle Kuma ni da bansan ma abinda ke faruwa ba. A Daren ya wuce airport banma rakashi ba saboda na gaji ga bacci se kawai na kwanta Bayan munyi sallama. Washegari ya kasance duk hada Kaya ne, ranar Monday da sassafe karfe shida jirgin mu ya tashi zuwa Malaysia Dan se mun fara trans in acan kafin Kuma mu wuce gida wato Nigeria. Abinda yafi min dadi a wañnan tafiyar kasancewar dukka zamu hadu acan su Rooks ma sun riga da sun wuce. Agogon hannun shi ya kalla sannan Kuma ya samu guri ya zauna gefen Ummiey wadda ke kallon duk wani Abu da yake Yi, daga ita se shi a gidan Dan Nads da Harith sun tafi gidan su Rooks sarki da Daddy Kuma suna fada. Ummiey ta dube shi tace " Yaushe ne saukar su Afiyya din? Na zata zakaje Kano taho dasu" Yayi dariya yace " Ai Kawu Tijjani zai dakko su shiyasa" Ta gyada Kai tace " So da kaje Lancaster kayi Mata magana akan Hasher dinne?" Ya girgiza Kai yace " Ni ban Mata ba, bana son taji maganar a bakina Amma munyi magana da Mummy da Kuma Uncle Babawo yace min wai wannan tsohon mijin nata shima yazo Wai da family dinsa..." Da sauri Ummiey tace " Wai Junaidu? Amma ma dai a gaida Tijjani me karfin zuciya shi wannan yaron har ya Isa ayi Masa second glance." With lot of humor a muryar Shehu yace " Ummiey ni nasan afiyy ba zata taba zabar wani miji Bayan ni ba, so shiyasa banma bi takan maganar ba shi Kuma Hasher yayi contacting Dina akan maganar nace Masa ni bazan Yi fada da kowa akan ta ba nasan idan har ita zata zaba mijin ta Bata da wani se ni se Kuma idan Allah ne Bai nufa ba" Ta Dan bugi kafadar shi kadan tare da gyada Masa Kai tace " You have so much faith in her" Yayi murmushi Yace " I believe in her Ummiey" Ta musu adduoi sannan ya wuce daki Dan ya huta kafin karasowar su Afiyya. Karfe Tara na dare muka shigo garin Ringim, tun daga gate din legal nake ta kalle kalle ko Ina se Ina tuna memory that's lingered a wañnan gurin, har seda muka shigo cikin gari mukai parking kofar gidan da yake mallakin na uncle Babawo ne. Shekara biyu kenan da na bar garinnan gashi na Kara dawowa, sede I'm no more that naive girl wannan din wata sabuwar yarinya ce wadda ta Kara fahimtar rayuwa da Kuma zaman duniya. Muka fito zuwa ciki a matukar gajiye, Ina shiga nayi daki na fada Kan gado ko veil Dina ban cire ba, nayi shiru Ina lumshe idanuna a take kuwa bacci yayi gaba dani, nasan Ina baccin naji shigowar Mom da Nanny Amma banji fitar su ba, se Sha biyu sannan na farka idanuna har lokacin akwai bacci, na tashi na gyara kwanciyata na cigaba da bacci. Washegari da wurwuri mukai gyaran gida komai ya koma muhallin shi sannan nayi wanka naci abinci na koma daki ko wayata ban nema ba na sake komawa bacci. Wajen daya na farka nayi sallah sannan na fito parlor nayi kicibis da Nads da Rooks, suka yo kaina kamar zasu kayar Dani na fara musu ihun su sake ni Zan Fadi kafin Kuma na zauna " Mom dinki ta fita tun dazun kema tashi zakiyi mu tafi" Nace " Ina zamuje?" Nads race " Gidan Ummiey mana!" " Ummiey fa? A'a wallahi bazan je ba" "Kunyar surukai!" Na wuce daki na canja Kaya sannan na fito muka fita, iska na kadawa a hankali muka nufi gidan Mummy kamar yadda nace musu sede da mukaje Bata gidan, na Ciro wayata na saka Sim Dina na Nigeria sannan muka fara Hira se tsokana ta suke Wai jikin su na Basu kafin a Gama hutunnan zaayi min aure. Nayi dariya nace " Da an rage min wahala wallahi dama so nake na kasance da Honey kullum" . Rooks bakin ta kamar zai yage Dan mamaki yayinda Nads ke fadin " Lallai in law kice a matse kike" Na Harare ta " Ke Nads I'm your elder sister yanzun stop teasing me" Kafin ta bani amsa wayatta tayi ringing ta dauka Babu jimawa ta dubeni tace " Dad dinki na Neman ki acan gidan Waziri" Nace " Toooo!" Na mike Ina musu kashedin su jirani na dawo sannan su sayo Mana Dan malili muci idan na dawo se suka ce kawai idan na Gama na same su a gidan mu can zasu koma. A hankali na cigaba da tafiya har nazo kofar gidan Kawu Sa'idu, na tsaya ba tareda na shiga ba Amma se kallon zauren gidan nake rayuwa kenan. Komai ya wuce se tashin labari,na tuna lokacin da nake ganin rayuwa ba zata taba komawa daidai ba, na tuna lokacin da nake ganin Babu wani Jin Dadi a rayuwa , lokacin da nayi giving up akan rayuwar ma Baki daya lokacin gani nake banida wani hope na kara samun yancin but Allah ya nunamin shike da iko bani ba. Na juya na cigaba da tafiya nayi niyya Zan Shiga Amma ba yanzun ba se na dawo daga Kiran Dad. Na danyi nisa kadan naji muryar Hafsisi tana kwala min Kira, a sukwane na juya ita din ce kuwan da Sahib a hannun ta yaron Siyama, na saki murmushi lokacin da ta karaso tana fadin " Afiyya kin ganki kuwa?" Nace " Me nayi?" Tace " Innanlillahi se wani haskawa kike kin Kara kyau" Nayi dariya nace taje gida zanzo yanzun jirana ake, ta ruko hannuna tana tambayata kp da gaske zanzo nace Mata ai alkawari nayi.sannan na samu ta tafi ni Kuma na hanzarta naje. Shima gidan an gyara shi sede Ina iya hango guraren da mukai wasan kasa, guje gujen da komai, Allah sarki Hajiya kakata. Kofar parlon takalma me sunfi biyar hakan yasa gabana faduwa Amma na daure bakina dauke da sallama kaina Kuma a kasa na shiga, Mummy ta fara fadin " Mashaaa Allah Afiy xo nan" Na saki murmushi na Isa gareta tare da rungumar ta nace " Mummy Ashe kina nan? Ina wuni?" Ta amsa sannan na gaida Dad da Kawu Tijjani, Ina daga kaina Naga Kawu Sa'idu a zaune ya zuba min idanun shi, nayi saurin janye nawa na gaishe shi a ciki ciki kafin Kuma na Kai idanuna kan sauran occupant din, subhannallah! Kadan ne zuciayata Bata fito ba ganin Junaidu wani dattijo da Kuma wasu su biyu da ban San su ba. Gaban ya Fadi na dubi Mummy se Naga ta min alamar na gaishe su, bakina na Dan rawa na gaishe su, dattijon yace " Amina kece?" Na Dan gyada kaina kadan sannan Kuma na sunkuyar da kaina. Kawu Sa'idu Dake gefe yace " Tunda tazo se mu Basu guri Dan su sasanta kansu ko?" Da mamaki na dago cikin sauri na kalla Kawu Sa'idu, na kalla Junaidu da yaki dauke idanun shi daga kaina, se lokacin na lura da sauyi a tattare dashi, Naga wata irin nutsuwa da ban taba gami a tare dashi ba Amma duk ba wannan ba meye Kawu Sa'idu ke fada Haka? Ni da way zamu sasanta? Haba ba dai Junaidu ba wannan mafarki ne ma, mummunan gaske ma kuwa. Dad ya dubi Kawu Sa'idu yace " Ban zo gurinnan Dan na hada aure ba, nazo na bawa yata kariya ne, ni ne ubanta ni ne me hakkin zaba Mata abinda nake ganin ya dace da ita. Junaidu kace kana son ganin Afiyya gata Ina sauraronka" Naji dadin maganganun shi, naji karfin gwiwa da Kuma Jin Dadi a raina. Junaidu ya taso yazo ya tsugunna har gabana inda nake zaune ya dira gwiwar shi biyu a kasa sannan ya fara roko na na yafe masa, yasan ya cutar dani...bla..bla...bla... Tunda ya fara magana nake kallon shi, he seems moody, dukda dama bantaba ganin faraar shi ba Amma nasan da gaske shi din se a hankali, but yanzun akwai sabon Abu a tattare dashi. Kaina na girgiza nace " Duk abinda ka min, son ranka ne ban maka komai ba, Amma kayi min komai, Dan Haka yafe maka bakai zaka ce ba ni ce Zan gani idan ka cancanci hakan." Kowa yayi tsit nasan mamaki suke, Kawu Sa'idu ya fara kokarin magana Dad ya dakatar dashi " Right dinta ne idan taga zata yafe to? Ni bazan matsa Mata ba saboda ita kadai tasan wahalar da Tasha" Kawu Tijjani ya gyada Kai yayinda na dubi Junaidu he looks disturbed abin tausayi kawai Baki daya, da idanu na pleading I'm sure da su zaiyi amfani wajen plead din, na dauke kaina se naji muryar Dad na fadin " Ni fa na Gama magana ba zata koma gidan shi ba" Malam da se lokacin yayi magana yace "Aji ta bakinta tukunna" Dad yayi dariya yace " Afiyya Zaki koma gidan Junaidu?" Kafin ya karasa na girgiza kaina na Kuma bude Baki nace a'a Dole Haka Suka tashi Sika tafi sannan Dad yace min Hasher yazo musu da batun Yana sona, Yana son na nutsu sub bani kwana biyu na zaba ko Hasher ko Shehu, banma motsa ba kaina a kasa nace " Yaya Shehu na zaba!" Afiyya is not free pay 300 to A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258 59 Labban Dad sukai curving alamar sakin murmushi da yayi a ranshi Yana ayyana Afiyya my daughter, na kalli kowa naga yadda dukka suke kallona Mummy ma mamaki ne kwance a fuskarta Amma Kuma she looks impressed. Ka u Tijjani ya dubeni yace " Know that wannan din is final, ba Zaki zo kice wani Abu ba Kuma" Na gyada Kai na nace " Na yadda Abiey" Yace " Tashi kije" Nayi musu godiya fuskata dauke da murmushi na fito zuwa tsakar gidan Ina shakar numfashi me dadi, Ina jin tamkar nayuwa kaina babban zabi, se yau naji inada yanci da aka barni na zaba abinda nake muradi da kaina. Ina zuwa kofar gida Junaidu ya taso tare da nufo inda nake, ganin ya Sha gabana se kawai na tsaya tare da kallon shi fuskata a hade nace " Menene?" Yace cikin marairaice fuska " Amina ki bani dama Dan Allah na Kara Zama mijin ki a Karo na biyu, wallahi bazan Kara yin abinda nayi ba" Nayi mishi wani mugun kallo me cikeda tsana, I can't deny the fact that I hate him, seeing him makes me sick, irin sick dinnan fa, yanzun ma da nake tsaye dashi nasan se nayi zazzabi ko mura, nasan Rukayya Amin zatace samun guri, to Amma Rayyanatu tasan cewar ko lokacin Ina gidan shi bana son shi bana kaunar shi kawai Ina jurewa ne saboda a lokacin banida mafita, Kuma lokacin shi din mijina ne Dole na Masa biyayya! " Junaidu inaga baka ma fahimce ni ba ko? Ka kalla idanuna kaga me Nene a cikin shi. Ka sani wancan Lokacin da na zauna da Kai Babu yadda zanyi ne, ni idan ni ce Kai emphasizing zanyi akan na yafe maka Amma ba Wai kokarin maida ni ba, ni din na maka nisa" " Amina Dan Allah ki bani dama na gwada Miki yadda son ki yayi tasiri cikin zuciyata, a dalilin ki na gyara halayena..." " Ina maka murna" Na fada Ina waving hannuna me wayata a rike, juyawa nayi na wuce Dan na gaji da Jin maganganun shi. Har na like Yana tsaye Yana kallona yayinda nake tafiya cikin nishadi da farin ciki. Wayar shi Dake cikin aljihun shi ta fara kara alamar Kira ya shigo yayi saurin Ciro ta sede number ma baayi saving dinta ba, ya kura ma lambar idanu kafin Kuma ya dauka Yana sallama se Kuma ya Kara marairaice fuska Jin muryar Safiyyu, " Mutumin se ka fito ka bace a duniya! Ko tambayar wanne Hali nake bakai ba" Safiyyu ya fada cikeda nishadi, Junaidu yayi wani furza yace " Ba kanta fa alamura sun rincabe anan din" Cikeda rashin fahimta Safiyyu yace " Me ya faru? Badai wani abun bane Kuma" Junaidu ya Dan jinjina Kai yace " Akan Amina ne..." " Wacece Amina? Tukun yaushe ka Bari har mace ta Shiga rayuwar ka har kake tunanin ta. Kaga wannan maganar mu hadu a kazaure kawai" Ya kashe wayar, Junaidu yayi shiru yana kallon wayar wani irin azaba yake ji cikin zuciyar shi, gani yake matsawar Afiyya ta kubce Masa to zauce wa zaiyi, Dan Haka yake ganin kawai zai amsa tayin zuwa ya hadu da Safiyyu, Dan yasan zai sama Masa shortcut din komai. Ban Jima ba na karasa gidan mu, tun daga gate nasan Hafsisi da Mino na gidan, Nima da farin ciki na na shiga bakina dauke da murmushi, a tare suka zo suka rungume ni Ina yin sallama, Nima na rungume su, seda muka zauna Nads tace " What a reunion" Nayi murmushi na zauna muka gaisa nace " Mino Ina Siyama? Ita ya bata zo ba" Ta tabe bakinta tace " Tana gida auren ta ya mutu" Na jajanta musu da gaske har Raina banji dadi ba, mun Jima muna Hira kafin Kuma Suka min sallama Suka tafi, na dawo wajen su Rooks a daki na zauna Ina kallon Nads nace Mata " Nads Kan Yaya Hasher daya yake kuwa? Me yasa zaije yace Yana Sona Bayan na fada Masa Honey nake so" Nads ta kalla Rooks tace " Ke Baki San waye Yaya Hasher ba, su fa Haka Yan gidan su suke. Kinsan brother din shi Ya Hussein Haka ya so Yar Anty Ya Kaka, do you remember her?" Na gyada Kai na, ta cigaba da fadin " Asiya wadda ta fada mishi ita tana da Wanda zata aura Amma da yayi blowing maganar a family seda kowa ya fara ganin laifin ya Asiya har yau zancen da nake Miki Basu shiri" Nayi tsaki nace " Tabdi ni Kam I'm no match for that nonsense, ko a gaban waye zan fada nace Honey.." Ban ma karasa ba Sega wayar shi ta shigo, na saki murmushi me ainahin kyau daga karkashin zuciyata na dauka " Ni nayi fushi ma! Tun jiya baka neme ni ba" Ya Dan marairaice fuska yace " I'm sorry my Darl! Kin dawo a gajiye nasan kina bukatar hutu shiyasa. Where are you? Can I see you?" Na kallesu kowacce hankalin ta akaina yake nace Masa Ina gida , se yace to zai zo zuwa yamma. Babu jimawa Mom da Dad har Nanny Suka dawo, Dad ya kirani dakin shi gashi gani ga Kuma Mom yace " Can you find a soft place a zuciyar ki ki yafawa Junaidu?' Na gyada Kai yayi murmushi yace " Can I ask a favor?" Na sunkuyar da kaina nace "Babu favor Dad, just order me I'll comply" Yayi murmushi na Jin Dadi yace " Zanyi fixing date din aurenki kafin mu koma Lancaster, saboda wannan abubuwan sun fara damuna, bana son yadda kowa ke cewa Yana son ya aureki" Na Dan kalleshi saboda abin yazo min a bazata ban Yi planning aure kwana kusa ba, Amma ya zanyi hakan yasa nace " Dad duk yadda kayi is ok!" Ya gyada Kai yace " I'm sorry yazo abruptly, mutane na threatening position din Shehu, so zamuyi magana dasu duk yadda ake ciki Zaki jini" Na gyada Kai na fita na samu Rooks zasu tafi gida hakan yasa Mom tace na bisu tasan Zan Dan ji dadi, Babu musu na bisu Amma se na kasa fada musu abinda aka ce. Muna zuwa mummy ta Gama girki tasa aka zuba Mana ta zaunar damu muka ci kafin ta kirani dakin ta * Hope baa takura Miki ba zancen auren?" Na girgiza kaina nace " A'a Mummy kawai banyi expecting din shi close Haka ba" Tace " Eh, muma ba Haka muka so ba, Kinga shi Shehu ba yaro bane, na tabbatar aure yake so but Yana Kara ne, idan ma Istanbul zaku zauna we can transfer you makarantar ki can, se Kuma Kinga Junaidu har yanzun ban aminta dashi ba ke har Sa'idu they can do and undo,dukda muna addua Amma ya kamata mu Zama wary of them. Kiyi addua nasan banida matsala da Shehu Ina Miki fatan farin ciki me daurewa Afiyya, Inshaaa Allah burin mu na ganin rayuwar ki ta inganta ya a dab da cika" Ta fada tana bude hannunta Babu musu na shiga ta rungume ni, se naji na Dan ji sanyi a raina, Kuma Nima Ina hango idan baayi auren ba kamar na shiga hakkin shi da yawa, all what matters to me shi ne naga Yana farin ciki. " Nadia ya na ganki ke daya Babu Rukayya balle Afiyya" Ummiey ta fada lokacin da Nads ta koma gida ita daya, ta cire veil dinta ta aje ta dubi Shehu da ya fito rike da hula me glass, Yana sanye da wani yadi me laushi fari tas hatta aikin da akai fari ne, hannun shi ya samu ado da kyakyawan silver agogo, fuskar shi Banda annuri Babu abinda take fitarwa, ya karaso Yana jin Nads na fadin " Rooks zatai bako ne, ita Kuma Afiy kinsan Yaya Shehu dai ya rabaki da yarki" Shehu ya kalleta kamar yadda Ummiey ke kallonta " Ban gane ba" " Ba kace zaka aureta ba, tana can kunya takeji. That girl should be sent back to 18cents. She's too local" Se Jin duka tayi a hannunta yace " Afiy yayarki ce, you should know this" Ummiey ta mike tana fadin " Zo mu tafi, I need to see her" Shehu yace " Wai Ummiey Ina Zaki? Gurin Afiyya Wai?" " To da Ina? Kasan yaushe rabon da na ganta?" Ya Bata Rai sarki na ta dariya yace " Ummiey Zaki Bata Masa shiri, ki Bari gobe se kije kawai" Ta dauki mayafi tayi gaba tana fadin " Sede shi ya fasa, Ina son azo a tukani" Shehu ya kalli sarki yace " Bro talk to your mother naaa" Sarki ya kwashe da dariya yace " Man just follow her kasan ba ji zatayi ba!" . Afiyya is not free pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258.60 Duk wannan fara'ar da murmushi duka suka dauke yayi kicinkicin da fuska shi a Dole ta takura Masa, ita Kam Ummiey ko kallon shi batayi ba a ranta tana ayyanawa lalali Shehu ya girma, she battled with him akan ma ya yadda yayi budurwa lokacin Kuma da yayi budurwar se Kuma tazo a wadda Babu Wanda yake kallon ta dace ayi soyayya da ita. Ta sauke ajiyar numfashi tana fadin yanzun Sarki ya rage dukda shima ya tsayar Amma Kuma family yarinyar na ta Masa Wasa da hankali, Dan dai kawai Bata son shiga irin wannan shirgin da zata ce kawai ya hakura ya nema wata. Kallon shi tayi lokacin da yayi parking kofar gidan mu, ya dubeta fuskar shi a sake, shi Haka yake Bai Faye fushi me tsaho ba yace " Ummiey muje" Ta fito sannan ya rufe motar Yana baya tana gaba, ni Kuma Ina daki na na Gama shiryawa cikin wani Jan material me tsantsi, jikin shi anyi embroidery da green din zare na kananan flowers. Dinkin riga da skirt. Inata kokarin daura dankwalin Amma tsantsin shi ya Hana ni na daura. Se kawai na dakko veil na yafa tun daga kaina Dan ya rufe bakin gashina. Body mist Dina na fesa sañnan Kuma na dauka wayata Dan fitowa Jin kwalla min Kira da Mom keyi, na samu na fito kafata sanye da wani flat shoe green Wanda aka Masa ado da clear Crystals a jiki. Ina fitowa mukai Karo da ita alamar gurina zata zo, nayi saurin ja baya ta dubeni tare da maida ni daki tace " Ina kallabin ki yake?" Na nuna Mata nace " Na kasa daurawa yayi tsantsi da yawa" Ta girgiza Kai tace " Come let me help you, ya kamata daga yau ya ganki cikin kyawun yanayi saboda yau dinne akai officiating relationship din ku" Ta fada tana daura min dankwalin in a turban wrap, na kalla kaina Naga yadda nayi kyau na saki murmushi nace " Amma an fada mishi cewar auren is close?" Tayi dariya tana kallon fuskata tace " Su Suka nema ai, dama Uncle din ki na kokarin yin hakan se Kuma Suka ce suna so" Na gyada Kai nace " School Dina fa?" Ta mike tace " Idan yazo feel free ki tambaye shi duk abinda kike so , ok?" Na gyada Kia ta fita tana fadin na zauna idan yazo zata saka a Kira ni. Wayata na dauka Ina karawa a kunne saboda Kiran da ya shigo, Yaya Hasher ne, mun Jima bamuyi magana ba dama Kuma Ina son Kiran shi naji yaushe na Masa alkawarin aure kamar yadda ya fada. A dakile yake magana kamar Wanda akai Masa Dole hakan yasa nima na amsa kamar irin ya dameni dinnan. " Afiyya yanzun ke Baki ji kunya ba a tambaye..." " Sorry I've to go Ina da baki" Na fada tare da sauke wayar daga kunnena na dubi Nanny dake tsaye nace " Nanny nayi kyau kuwa?" Bakinta dauke da murmushi tace " Sosae ma kuwa. Afiyyata ta girma gashi har zatayi Aure. Allah ya albarkace ki" Na karasa na rungume ta nace " Amin Amin uwata ta kaina" Se ta fara dariya tace " Sakeni kije Hajiya Mariya na jiranki" Na juyo da mamaki nace " Ummiey Kuma? Me yasa tazo?" Bata bani amsa ba Mom ta fara kwala min Kira, na bubbuga kafata nace " Bata San kunyar ta nake ji ba ko?" Na fita kaina a kasa , tana zaune kamar kullum cikin lace anyi Masa dinkin bubu, she looks expensive like always, na kalleta kafin na Kara maida kaina kasa nayi sallama sannan na tsugunna gefen ta tayi saurin dago ni ta zaunar gefen ta tace " Haba Afiyya ta Yaya Zaki dawo Baki zo kin gaishe ni ba, I'm hurt Afiy" Mom tana murmushi tace " Ai me Borno ya shiga tsakanin ki da yarki fa" Ta gimtse fuska tare da fadin " Kowa Haka yake fada min Maman Afiyya, gaskiya ni bana son Haka. Afiyya I'm your mother kinji? Ki saki jikin ki Dani" Na gyada kaina na gaishe ta ta amsa sannan tace min " Tashi kije gurin shi, I need to talk to your mom" Na gyada Kai na sannan na silale na fice, Yana tsaye Yana kallon entrance din alamar Yana Jirana, Ina zuwa ya saki murmushi Yana fadin " Here comes the Queen!" Na saki murmushi, Ina ganin watarana idan dariya da murmushi zasu Kare to tabbas nawa zai Kare, hardly na hada idanu dashi banji Murmushi ya kubce min ba, he gave me every reason to smile and laugh, kusan dukkan abinda nake so Yana kokarin ganin yayi min, in fact we share and understand the same love language. Na karasa inda yake nace " Ni nayi fushi da Kai fa" Ya shafa fuskar shi yace " Tun dazun nace kiyi hakuri fa. Kinga yadda kikai kyau kuwa. You're putting the stars to shame fa" Na saki dariya Ina daga kaina na kalli kyawaawan taurarun da Suka kawata sama nace " Am I that beautiful?" Yayi murmushi ya dawo gabana ya tsaya yace " You're beautiful, you're perfect Baby, I love everything about you" Na rausayar da kaina Ina jin wani Abu Yana Kara shiga cikin zuciyata zuwa jinin jikina, I found myself falling for him. Wannan lokacin bamuyi ma hirar da mom tace ba se soyayya kawai da mukai, sede lokacin da muke Hira nake spotting wayar shi na haske saboda ya aje ta a saman mota, sunan da akai saving ya fara da NU ya Kare da BA. Banma nuna masa na gani ba saboda I'm really enjoying the moment. Seda Ummiey ta fito sannan mukai sallama Suka tafi. Ina dawowa na wuce daki ko abinci ban nema ba. Na cire kayan jikina Sega Mom ta shigo da waya a hannun ta Wai zamu zaba furniture, na marairaice fuska nace " Can we leave it zuwa safe Allah na gaji" Se ta gayda kanta kawai ta yimin sallama, na dauki wayata na fara Kiran shi Bai dauka ba ya katse ya kirani " Har an fara kewata?" " Wacece NUSAIBA? Is she that same lady?" Na tambaya Ina tsatsare shi da idanuna, ku kwace wallahi Yana gabana. Ya sassauta murya yace " Damsel ki tsaya kiji" Nace " A kwance nake Kuma shi ne dalilin da yasa na kiraka, I want to know who the hell she's, wannan Karo na hudu Ina tare da Kai tana kiranka, fada min wacece ita" Jin muryata ta fara sama na tashi na zauna shi dinma se ya fara lallabani " Ai na Baki labarin ta, she's in the past Damsel..!" Nayi dariya nace " Ok yanzun ma daga past din take Kira kenan? See Honey gaskiya idan you over her tell her karta Kara kiranka idan ba Haka ba ni Zan fada Mata" Ko ta Ina zan iya? Waya ga cika baki a gurina, seda na tabbatar na hargitsa shi na Kuma saka Masa a zuciyar shi ni ba wawiya bace and I'm not into such nonsense sannan na kashe wayata gaba daya. A wañnan yammacin Junaidu ya koma Kazaure, Yana zuwa ya Kira Safiyyu Wanda yace su hadu can wani guri gaba da Shaiskawa, Haka ya Niki jiki ya tafi har zuwa can ya sameshi a zaune shi daya. Bayan sun gaisa ya dinga Masa dariya Wai me yeya koma wani kamili, shidai Junaidu ya dakatar dashi ya fada Masa ainahin abinda ke faruwa Safiyyu yace a washegari zaije maradi ayi ta ta Kare. Junaidu ya tafi dukda Yana jin Anya yayi hakan ko dai ya Bari yaga abinda Allah zaiyi Amma Ina yasan aikin Safiyyu kamar yankan wuka take! Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258 Afiyya is not free pay 300 to A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258[24/02, 13:22] +227 98 36 59 34: 61 Junaidu ya samu abun Hawa ya nufi gidan su Dan Hajja tun Yana Hanya take Kiran shi akan ya Suka ji shiru Bai dawo ba, hakan yasa suna rabuwa da Safiyyu ya nufo gida, Amma se yake Jin cikin zuciyar shi kamar abinda yake Shirin aikatawa ba daidai bane. To Amma ya iya ya ayyana a zuciyar shi zai cigaba da Zama da kuncin zuciya ne, Afiyya ita ce hasaken da ta shigo cikin rayuwar shi ta haskaka wannan duhun da ya mamaye shi, uta din ce ta fitar dashi daga kangin wahalar da yake ciki, to Kuma shi din me zaice tunda Afiyya ta nuna bashi take so ba bashida wani zabi sede ya dauke ta daga abinda ya hanata ganin shi. Ya karasa gida ya samu su har gumin tafiyar su ya tsane, ya rasa yaushe yarinyar nan Afiyya tayi bakin kallon shi, yaushe ta daina tsoron shi da har zata kalla idanun shi tace Bata son shi wannan Abu ba karamin mamaki ya bashi ba, yayi shiru tuni yadda ta Zama budurwa sosae tayi kyau, duk yadda yake ganin kyanta da komai yanzun yaga ta kere da, ta Zama babbar mace wadda maganarta ma is reformed . " Yaro tunanin me kakeyi? Inata tambayar ka ya kukai da Aminatu din?" Ya dawo daidai sannan ya dubi Hajja a marairaice yace " Bata yarda ba ta Kuma ki yafe min". Hajja ta gyada kanta cikin tausayin Junaidu tace " Dama hakane, ka Bata lokaci har ta samu ta yafe maka, se Kuma ka fara nuna Mata sonta da kakeyi da gaske. Abu na karshe mafi amfani ka cigaba da addua, idan ita alkhairi ce Allah zai baka ita idan Kuma akasin hakanne to Allah zai saka maka dangana a zuciyar ka" A ranshi yace Ina wani dangana Hajja? Dan dai Baki San yadda zuciyata ke min bane da Baki ce hakan ba. " Hajja aure fa zasuyi Mata" " To ya zakai, se kayi hakuri ka duba wata ka aura, dama Allah baiyi dogon Zama a tare daku ba" Duk yadda ta dinga lallashin shi da nasihu iri iri se yaji Kuma zuciyar shi tayi taushi, mussamman da yaje yin sallar ishai Bayan ya idar malam ya daura Masa karatu, a ciki ya nuna Masa dukkan abinda ya samu bawa to da sanin ubangijin shi, Kuma cikar musulmi shi ne ya yadda da wannan kaddarar me kyau ko akasin hakan. Se yaji Anya bazai bar Afiyya ba, shi din ta Yaya akai ya cancanta ya aureta? Ya manta dukkan abubuwan da yayi Mata, ya dubi hannun shi ya tuna abubuwan da yayi Mata da wannan hannun nashi me Kama da katako, ya tuna Mari, duka , zagi, kulle da Kuma rashin Bata abinci dukda gara da aka kawo Masa daga gidan su Amma se ya siyar ya Kara jarin drugs dinsa da yake safara. Ya dafe Kan shi ya rasa abinda yake damun shi, ya riga ya Bata komai baya tunanin wani me hankali me Kuma zuciya zai ma sparing Wanda ya Masa Haka second glance. Ko shi dinne tabbas ba zai yafewa ko waye ya Masa Haka ba. Dan Haka ya kamata ya kyalle Afiyya Bai cancanci Zama da ita ba kamar yadda Yaya jamilu ya fada Masa da Kuma kawunta da take hannun shi, ya fada Masa ko Afiyya ta rasa miji ba zai taba aura Masa ita ba, Kuma Koda Afiyya na son shi. Dan Haka ya lalubo wayar shi ya fara neman layin Safiyyu Dan dakatar dashi daga aikin, Amma Kuma se wayar taki Shiga, ya Kara Kira Amma still wayar Bata ma magana sede kawai ta dauke. Ya saki nannauyar ajiyar zuciya ya koma ya kwanta Amma a wañnan Daren Bai runtsa ba. A bangaren mu shirye shirye sun kankama wanda har mamaki abin yake bani, saboda ku zaku ce dama can sun hada bikin ne, ba zaka ce irin short notice wedding bane. Kowa bangaren shi kokarin shiryawa yakeyi. Da farko bayan munyi wannan fadan Akan that Nusaiba se Naga meye Kuma na Bata lokacina akan ta, tunda ni ya zaba ni yake so se na kyale shi. Dan Haka kafin ma ya Kira ni da safe na kirashi, ni na tashe shi a bacci, muka Yi Hira sannan ya tambaye ni " Kina son Lancaster ko Istanbul?" Na danyi shiru na dakiku kafin nace " Saboda school na zauna a Lancaster din ko?" Yace " Duk yadda kike so, Amma inaga sede jibi na koma gurin aiki Naga idan zasu iya min transfer zuwa firm dinsu dake can" Nace " To hakan yayi, Amma me Ummiey tace?" " Ummiey doesn't have business with this, rayuwar mu ce mu n zamu tsara yadda zamuyi ko?" Na gayda kaina sannan mukai hira se Kuma mukai sallama yace na fadawa Mom zai fadawa Daddy da Ummiey da Kuma Dad dina. Ina fitowa na fadawa Mom tace maganar da suka Gama Yi kenan da Mummy hakan yafi sauki akan ace ni Zan bishi. Kafin dare an Gama deciding Dan Haka washegari ya tafi abuja, the next day ya wuce turkey. Anan aka fara shiri sosae da sosae kowa nashi bangaren. Akwai wata Anty na kanwar Mama, ita ta taho daga maid tazo gyara min jiki, sunanta Anty Falmata, Kama muke Sosae da ita. Ranar da ta karaso Ringim a gidan Ummiey ta sauka seda tayi wanka ta shirya sannan Harith ya rako ta gidan mu, an Gama Mata komai na Shirin tarba, Ina kwance ka kujera a parlor Ina kallo ta shigo, na Mike na zauna shi ne karon farko Dana fara ganin ta, wancan time din Bata zo ba mijinta ba lafiya, daga nan baa fi wata biyu ba se ya rasu, Bata taba haihuwa ba dashi, a lokacin Ummiey tasa na kirata na Mata gaisuwa, shi kenan muke gaisawa, she's one of my best aunties da ko kwana biyu taji ni shiru she will check on me. Mahaifin su Mama nada Mata hudu. Maman Mama bama Yar Nigeria bace ance she's Ethiopian, Kuma Mama kadai ta Haifa ta koma can Ethiopia Amma ance da ciki a jikinta ta tafi, maman su Ummiey yaran ta bakwai, hudu maza uku Mata, Ummiey ce ta uku se Anty Falmata ta auta. Se wadda Bata taba haihuwa ba se kuma me Yaya shida ita ce wadda ta rike Mama a gurin ta. Ita ce mahaifiyar Anty Bintu maman Yaya Hasher. Dukkan su bazan iya tuna su ba Dan rabo na dasu tun Abbu da ya kaini, Haka Kuma dama kowa yasan ba nemana sukai ba se yanzun ne nake sabawa dasu. Ko wancen auren kadan Suka zo saboda Ummiey tace da Mummy Bata son suzo su ganni a wañnan halin, Amma wannan auren ni kaina nasan it's going to be grand. Na taro ta, Harith na ta min tsiua Nanny tana shigar min, na gaida Anty tace " Dama Babana (Shehu) yace Baki Kama da Anty Halima Dani kike Kama. I'm really sorry Afiy for dumping you. Bansan me ya hau kanmu ba" Nayi murmushi nace " Kai Anty!" Ni na Kira Mom wadda ta kule a daki se order takeyi, Suka gaisa tace a dakinta zata zauna Nima na kwaso kayana na koma can, Haka mukai a ranar aka fara shafe shafe da turare. Ana gamawa kafin yamma kuraje sun fito min akan fuskata Wanda response ne na rashin sabo. Yaya Sarki ta Kira Yana specializing akan dermatology ya min prescription. Gaba daya bayan an Gama komai aka tsaida date din bikin da koami wata daya. A cikin wannan watan se naji ko fitsari nayi Kamar kamshi yake, mura kullum nakeyi saboda turarruka. Amma Kuma nayi kyau na canja tamkar wata sabuwar halitta, jikina santsi da glowing kawai yakeyi. Se ana saura sati biyu sannan ya dawo. Anty Falmata na bacci nayi wanka na shirya cikin wani lace me kyau, na bude powder Zan shafa naji muryar ta tace " Don't break the rules!" Nayi saurin ajewa na fara dariya ta taso tace " Ya dawo kenan! Nayi Masa farin ciki da zai aureki, you've a golden heart Afiyya Wanda duk Wanda ya zauna dake se soki. Haka Ya Halima take, Haka Kuma Abbun ki yake. Continue been good ok?" Na gyada Kai sannan ta sallame ni na fito, Yana zaune ya Dan fada saboda he has been busy seda yayi reporting Lancaster sannan ya samo gida da taimakon Baban su Sheriffa da Dad daya koma can attending ma business. Na karaso inda yake zaune na zauna se naji kunyar shi nake ji, na Dan sunkuyar da kaina yace " What! Kunyata Kuma? No please karkiyi Haka" Nayi murmushi muka gaisa sannan muka fara Hira ya fara fada min yadda aikin da komai ya kasance dukda na sani tunda kullum se munyi waya ya bani labari, gidan ma seda muka zauna muka planning irin Wanda muke so kafin Kuma muka zaba. AFIYYA is not free pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258 [24/02, 13:22] +227 98 36 59 34: 62 Ana saura sati biyu biki da daddare na fito daga toilet nayi alwala Dan yin sallar ishai, wayata Dake aje Kan dressing mirror ta fara haske Dan a silent take. Na karasa na dauki wayar Naga Honey ne. Na dauka tareda karawa a kunne na, muka gaisa sannan ya sanar min idan sun idar da sallah zasu shigo shi da Daddy. Jin da Daddy ne yasa nace " Lafiya?" Yayi dariya kadan yace " I dunno. Inaga Yana son yaga yarinyar da zata dauke Masa Dan sa ne" Ya fada sounding playful, na Bata fuska nace " Kai ko? Ni sallah zanyi" Na kashe wayar Ina murmushi Nima, seda na idar sannan na fito zuwa dakin Mom na samu suna Hira itada Anty Falmata, na zauna sannan nace Mata " Wai Daddy ne zai zo" Ta kalleni tace " Wanne Daddy?" Nace " Daddyn su Nads" Duka seda suka tambayi lafiya, na girgiza Kai alamar Nima ban sani ba, Anty Falmata ta mike ta dakko min Kaya ita Kuma Mom ta fita ganin yadda parlon yake. Baa fi mintina goma ba se sallamar yaro akan suna so ayi musu iso, kafin Anty Falmata ta fita se gashi sun shigo da Dad da Kuma Abiey. Honey da Yaya Sarki na bayan shi. Seda Suka zauna Mom ta kawo musu drinks Yana ta dariya Yana fadin " Haba dai kamar bako? Dan Allah karki da naji kunya" Sukai dariya sannan suka gaisa da Nanny Yana ta Mata cewar ko ganin ta baayi, ni Kuma Ina daga daki Ina jiyo su, I never thought Yana Wasa haka, saboda shi Bai Faye Zama kamar Abban su Rooks ba, duk da dai dama nafi sabawa da Abban Rooks akan shi. Na fito tare da Anty Falmata, na je har gaban shi na tsugunna na gaishe shi, ya kalleni sannan ya kalli Shehu yace " Da ba Haka take gaishe ni ba, she always greet me cheerfully. Me Borno what have you done?" Kowa yayi dariya sannan ya dubeni yace " Uwata tashi ki zauna kinji? I'm still your father" Na tashi na zauna a kasa kamar yadda Naga Yaya Shehu da Yaya Sarki sukai, na gaida Abiey sannan Daddy yace " Nasan duk kunyi mamakin kiranku da nayi ko? Ba wani Abu bane kawai Ina son na Dan Kara taunasara da Me Borno da uwata akan muhimmancin addua. Nasan wannan yaron Junaidu ya dawo Neman aurenta kafin Shehu yayi winning, kunsan wannan jarabawar Allah ce? Allah ya jarabce shi da sonta Dan ya gwada imanin shi da Kuma karfin shiryuwar da yayi. Abinda mamaki suddenly yaro ya dawo Kan hanya, se Kuma ya dawo Yana son abinda ya wulakanta, ya daka ya muzguna ma, da kanka Baban Afiyya kace ka yadda da son da yake Mata, it's boldly in his eyes ko? To wannan yaron zai iya komawa ruwa yayi duk abinda zai iya Yi Dan aurenta, ko ba Haka ba? To shiyasa nake son mu hadu muyi addua iya karfin mu, farin ciki ya daure Mana cikin rayuwar mu Baki daya" Abiey yace " Wannan Haka yake Wambai! Tabbas Nima da abinnan nake kwana nake tashi. Muyi addua sosae saboda komai ya tafi daidai" Bayan anyi doguwar addua sannan Suka tafi Nima na zauna Abiey da Kuma Dad suka Kara nuna min muhimmancin abinda Daddy ya fada, na koma daki na cigaba da shirina, se hakan yasa na zauna na fara lissafo abubuwan da Junaidu zai iya yi. Saura sati daya biki aka kawo kayan lefena, acan gidan Waziri anan aka karba lefe na, se yamma sannan aka jibgo su cikin mota aka kawo gida, dakin Mom aka kaishi, ni dasu Rooks mukaje kalla, komai ka daga kasan bana Wasa bane, kayan sunyi kyau sosae. Se lokacin na Kara tabbatar wa tabbas da gaske auren zaayi. Bayan min Gama kalla Mom ta kirani daki anan na same Ammi Maman Basma, Mummy shikenan. Na zauna aka fara min fada ko nace nasihar aure wadda kusan duk tuni ne akan wadda Anty Nafisa take min kullum ita da Anty Falmata. Haka na zauna na saurara dukkan abinda Suka ce making a lot of mental note a cikin kaina, abinda yafi Zama min shi ne communication part, Ammi tace min Kar na sake muyi fada dashi na Bari mu kwana da wannan abin a raina, ko Yaya ne muyi magana akan abin, matsalar mu tamu ce mu kadai kada muyi involving wani har se abin yafi karfin mu. Idan min bar fada ya kwana ko Kuma muka ki magana akan shi, bayan Yana cin zuciyar mu to tabbas zaiyi drifting din mu apart. A cikin wannan satin komai na Shirin ya kammalla. Ranar Wednesday akai henna party, da farko naki yarda saboda bana son taron ma, Amma Mummy tace karya nake ban Isa ba Dan wannan shi ne banbancin wancan auren da wannan. Banyi kwalliyya ba Amma Banda glowing Babu abinda nake, friends Dina Sheriffa tazo, Maryam da Kuma Farha, Yan class din mu a UCLAN. Se yamma sannan aka Gama henna party wanda akai a gidan su Basma. Washegari ya tashi a Ladies gathering, a gidanmu mukai. Se ranar Friday da yamma akai Wushe wushe, tun safe sukai gaba, Nima wajen 10am yazo Ina daki Anty Falmata tazo ta kirani, Muna cin abinci da Farha su Kuma sauran suna harhada kayan su, Anty Falmata ta shigo tace " Shehu yazo ki Gama cin abincin ki fito ku tafi" Na dubi su Farha nace Mata " Anty su kuma fa? Duk acan zaayi musu make-up" Tace ai zaa tafi dasu mu fito Baki daya. Haka na bar abincin muka fito, daga ni seshi a motar se sauran motocin Kuma cousins dina da friends dina. Seda ya dauki hanya sannan ya dubeni " Damsel!" Na kalleshi sannan nayi murmushi nace " Honey!" Ya kalleni sannan ya maida hankalin shi Kan titi yace " Like play like play we're moving darl! Gobe zuwa zuhr inshallah kin Zama mallakina" Na kalleshi sannan na maida kaina gefe nace " I thought I've lost you duka, se gashi auren zai yiwuwu. I'm very grateful" Yayi dariya a hankali wadda seda tasa naji tsikar jikina ta tashi yace " No! Ni Zan gode Miki da Kika zabe ni Akan sauran mazan duniya. Inshallah Zan zame miki shugaba, aboki, Yaya, kani da Kuma baba. Inshallah Amina zamuyi Zama me dadi. Our home will be filled with love, laughters. Ina fatan Zaki bani hadin Kai" Na gyada Kai se ya harareni yace " Open your mouth and talk, Yara nawa Zaki Haifa?" Na kalleshi da mamaki yace " Tell me Mana" Nayi shiru kafin can nace " Biyu" Da mamaki yace " Biyu Kuma? Ki Kara uku su Zama biyar Mana" Na kauda Kai nace " Is not easy in labor room oooo!" Yayi dariya yace " Ai tare zamuyi sharing pains din, we're in together ko?" Na girgiza Kai nace ban yarda ba Amma na yarda mu Haifa uku, se yace zai San yadda zaiyi yasa muyi biyar din. Munyi Hira sosae a abinda Bai koa awa daya ba. Muna Isa dutse Sha daya nayi. Straight parlon din me Make up din muka je, ya dubeni yace " Tell her to be careful with this delicate skin of yours, gani nake ana tabawa jini zai fito" Na bude kofa Ina dariya nace " Kai ko! Waye ya fada maka. Bari ka gani" Na fada Ina mintsinin hannuna, ya runtse idon shi Wai ji take kamar jikin shi ake tabawa, nayi Masa dariya na wuce ciki. Karfe hudu I'm clad in asalin kayan bare bari su Kuma dukkan su sauran kawayena lafaya ce jikin su, wannan kitson gaban na al'ada anyi min shi tuntuni. Nayi kyau sosae da sosae. Tayi min pictures Haka me hoton da mukai hiring shima yayi min. Event din ranar yayi kyau ba karya, mummy da Ummiey sunyi kokarin gayyato friends din Mamana, Kuma sunzo su wajen goma, Banda matan abokan Abbuna Suma sunzo, ga manyan fans Dina Wanda Anty Azeema ita ce Kan gaba a kawo su, ko Ina na kalla se naji Dadi nakeji, tabbas wannan Karan nasan nayi aure da gaske. Se dare muka koma Ringim, a matukar gajiye nake Dan munyi dashi zai zo Amma yadda yaji muryata faint yasa yace nayi wanka na kwanta, tunda washegari will also be a busy day. Washegari ranar daurin aure, wajen Sha daya an Gama gyara min jikina, a wañnan ranar Kuma abokan shi sun hada Mana English dinner da daddare da zaayi a gidan Uncle din su nan a ringim. Lace na saka champagne color, komai da na saka champagne ne, ana Gama daura min dankwalin aka yafa min veil akaina naji an Gama daura aure, kawia se naji idanuna sun ciko da kwalla, wata rayuwar sabuwa Zan fara Kuma, ai tuni se hawaye ya balle min. Amina Abubakar ce kusa dani, me make up din tana harhada kayan ta, " Me ye Haka Afiyya? Kuka Kuma?" Da sauri me make up din ta taho tana rokona Dan Allah Kar na Bata fuskata Amma kamar zuga ni suke hawaye kawai nakeyi, duka suka tsaya suna kallona har nayi shiru sannan ta gyara min Amma idanuna yayi ja Haka ko magana bana Yi. Babu jimawa se gasu sunzo, tun daga nesa na hango shi all clad in white shadda da babbar riga, he looks Charming se murmushi da dariya yakeyi, har suka karaso mukai hotuna, Murmushin da yakeyi yasa na manta da wani duk insecurities na fara bude Baki Ina dariya. Ana gamawa Anty Falmata tasa na canja Kaya sannan aka kaini gidan sarki chamber kamar shi, ta kalleni ta tsufa se na tuna Hajiya kakata, yadda muke yawan zuwa wajen ta. Ta riko hannuna kafin a Fara budar Kan tace " A dakinnan na raini mustapha da Abubakar, saboda amincin su Mata ma Yan uwa Suka aura,tare sukai karatu. Gashi yau Allah ya nuna min Dan mustapha ya auri Yar Abubakar. Allah ya albarkaci auren ki ya jikan Dana" Ta karashe da doguwar addua akai formalities na karba ta sannan da daddare mukai Shirin dinner, shi kadai ne Wanda mukai tare dashi, suit ya saka kamar peach kamar nude Haka, shirt din ciki da tie dinsa were all Navy blue, ni Kuma na saka gown ta material me Dan glitters maroon, munyi kyau, friends dinmu duka sunyi kyau sosae. Bamu Jima ba sosae muka Gama sannan muka fito rakiya, yawancin Dana nan zasu kwana tunda dare yayi, hannun shi cikin nawa, seda duka Suka shiga mota suka tafi sannan ya bude min gefen shi na shiga ya zagayo ya tada motar tare da Kama hannuna ya rike cikin nashi. Dayan Kuma Yana driving har muka karasa kofar gida. Yayi parking tareda pecking hannun nawa Dake cikin nashi yace " I badly wanted holding these hands, I wanted feeling their softness. Da nayi hakuri gashi na rike" Na danyi kasa da kaina saboda caressing hannun nawa da yakeyi da thumb dinsa, Jin na Yi shiru yasa yace " Nasan kin gaji, the day was very busy kije kiyi bacci Amma ni nasan bazan iya ba, had it been Zan jiki a kirjina I will have a peaceful night!" Jin hakan na turo bakina tareda kwace hannuna daga nashi yayi saurin rikeni ya juyo da fuskata, for the first time naji bakin shi a cikin nawa. 63 Kana kallon yadda yake duba agogo tare da Kuma Jan tsaki lokaci zuwa lokaci kasan ya kosa motar ta karasa ta sauke su a kazaure, tun biyar na asuba yaje Tasha ya shiga mota, Dan malamin yace lallai lallai asirin da zaayi sede ya zamana Junaidu yayi da kanshi ba Safiyyu ba, gashi yau ne daurin auren Kuma Dole se ya kasance ayi binne binnen da Kuma hayakin Dole se de yayi da Kan shi kafin daurin auren. Yaso ace tun acan zaayi aikin da yafi kowa farin ciki, dama haushin Afiyya yake ji da danginta da sanadin su yaje har prison na kusan shekara daya, Dan Haka asirin da ya karbo ba Wai na fasa auren ne kawai ba, shima Junaid zaiji ya tsaneta bazai aureta ba sannan rayuwar ta se ta lalace gaba daya. Yayi murmushi Yana Kara kankame jakar da layoyin da Kuma itatuwan suke ciki, ya sake duba agogo yaga Sha daya da rabi gashi sun baro daura sun kusa kazaure abada. Lumshe idanun shi yayi Yana kiyasto yadda zaiyi fata fata da rayuwar Afiyya, Allah dai ya kaisu kawai ya ayyana a zuciyar shi. Suna Dan da Isa cikin gari wata Mata ta fara fadin driver ya tsaya yarinyar ta da Bata saka Mata diaper ba tayi Bayan gida, Kuma ya Bata har na kusa da ita. Dole driver ya tsaya Yana ta fadan ta Bata musu lokaci. Gashi acan extreme take seda kusan kowa na motar ya sakko sannan ta fito dan gyara yarinyar. Safiyyu ya bude idanun shi tare da kallon agogon wayar shi ya saki tsaki Wanda kowa ya gaji daji. Sauran passengers masu bukatar stretching kafafun su day Wanda zasu zagaya duka suka sauka se Safiyyu kawai ya rage cikin mota. Kamar bayan mintina biyar Babu wani Wanda ya Isa ya Fadi abinda ya faru, ko shi Safiyyu Bai Isa fadar yadda wuta ta fara daga jikin shi ba, shidai yasan ya fara jin burning sensation a jikin shi, ya bude murfin motar ya fito Amma wuta sosae ta kankama a jikin shi tun daga wandon jikin shi har zuwa rigar shi se ci suke tamkar Wanda aka zuba Masa fuel aka kyasta Masa ashana Haka yake ci, wani passenger dashi ya fara ganin shi ya saki ihu Yana fadin " Innanlillahi wa inna ilaihil rajiun!! Kuzo jamaa kuga ni" Safiyyu se ihun Neman taimako yake Yana kokarin yage kayan jikin shi Wanda hakan ke exposing jikin shi Yana Kara konewa. Ruwa Suka Nemo masu kasa ana ta zuba Masa Amma ko gezau wutar ba tayi ba, Haka suka tsaya kallon ayar Allah Dan kanta ta mutu ya zube a gurin jikin shi Babu kyan gani. NDLEA OFFICE, ABUJA. Files ne guda uku Wanda aka saka igiya aka daure su wani officer yake dauke dasu ya fito daga ofishin babban sashen zuwa nashi ofishin. Yana shiga nashi ya zauna tareda sake kallon sunayen da Kuma address din su duk da Suka Gama samu, ya dauki wayar landline dake aje Akan desk dinsa ya fara Kira. Bai wani Jima ba ya fara magana cikin turanci Wanda accent din barebari ke fitowa a ciki. A jikin desk din akwai sunan shi Muhammad Ali. A cikin magangun shi ya bada order Akan suspect din da ake nema masu trading hard drugs. Yana maganar Yana Kara bubbude files din sannan ya aje wayar tareda shafa fuskar shi, it was sure a hard job sunfi shekara uku suna Neman mutanen nan se yanzun aka samu aka San inda dukkan su suke. Junaidu na zaune kofar gida da wayar shi a hannu sunyi magana tun sassafe da Safiyyu Akan ya taho, dukda a lokacin da suke wayar seda ya fada Masa cewar shi ya fasa kawai ya barwa Allah ya zaba Masa abinda yafi alkhairi Amma Safiyyu yace Babu wannan maganar, aure se ya aura Afiyya ya jira shi Yana Hanya. Shi yasa ya fito kofar gida ya zauna, se wayar shi ta fara ringing a tunanin shi Safiyyu ne se yaga Malam ne abokin shi, ya dauka Yana fadin " Malam ka buya" Malam ya danyi murmushi yace " Gaba daya ka Bata ya maganar cocaine da mukai dakai zaa samu?" Junaidu yayi tsaki yace " Suna nan fa, akwai wajen 1kg a gidana ni so nake na daina harkar wallahi" Malam yace " Bari kawai zamuyi maganar yanzun kazo gidan Zan Aiko Yara su karba min" Daga Haka sukai sallama ya wuce gidan da se yayi sati Bai leka ba, Yana zuwa ya saka mukulli ya bude sannan ya Shiga inda shi kadai yasan gurin, ya fara Ciro cocaine din da wasu daga cikin hard drugs da yake dealing kawai se Jin alamar kyas din camera yayi, Yana dagowa yaji bindiga a forehead din shi, cikin sauri ya saki ledar tareda daga hannun shi sama in surrender, camera man din yayi snapping scene din Suka saka gloves suka kwashi kayan sannan suka handcuffing dinsa seda aka saka shi bayan motar su sannan yaga Malam a zaune ya zabga tagumi da tashi handcuff din, ya dube shi yace " Setup ne?" Yace " Ya zanyi?" A take ya mikawa Junaidu waya akan ya Kira abokin harkallar tasu. Gari ya waye tun asuba ban koma bacci ba Ina gurin Dad Yana Kara nausar Dani abinda ya kamata dukkan Wanda nauyi irin wannan ya hau kanshi abinda ya kamata yayi, nayi shiru Ina sauraren shi yace " Kiyi hakuri wannan gidan ba kamar wannan gidan bane, wancen you've every freedom Amma watarana zakiji kamar ke din captive ce, kamar a prison kike, nasan zaman da kikai damu Kinga yadda muke zaman mu lafiya da antyn ki, bawai bama fada ba munayi, but we face it together, kema Haka nake son kiyi. Ki sani nine babanki, ni din kullum Zan saurareki duk lokacin da kike bukatar hakan. Ina farin ciki da hannu na gida Zaki Shiga I'm sure of waye shi. Kada ki bani kunya, be the person I know you were. Please Afiyya" Na gyada kaina siraran hawaye na bin kuncina yayi min addua sosae sannan yace naje na tafi. Na dawo daki na tarar kowa na hada kayan shi Dan ranar kowa zai tafi. Na zauna Ina fadin " Meye kuke ta hada Kaya se kace korarku akeyi" Amina tace " Allah ya Baki hakuri" Na Mata banza na fita gurin Anty Falmata da Anty Yana Suka karasa gyara min jikina sannan nayi wanka na saka Kaya, wani lace ne me balain kyau , aka saka min sarka da dukkan wasu abinda ya dace Amma fuskata Babu ko powder Dan na tashi kuraje sun fito min Wanda Anty tace saboda makeup din da akai min ne, fuskata Bata Saba ba. Mom ta dakko wani set din sabulu, bridal set ta bani tace " Ki fara using dasu friend dita take siyarwa Nima dashi nake amfani ba karamin kyau ne dashi ba" Na kyabe Baki Ina kallon sunan Fattyjet 3D bridal set a jiki. Na amsa da to sannan aka saka min a kayana. Wajen Sha daya motocin da zasu kaimu airport mu tafi maiduguri Suka zo, ai se na fara kuka na kankame Mummy dukda duk tare zamu tafi, ta rike hannu na muka fito inata kuka har ta saka ni mota sannan ta zauna gefena, se babbar yayar su Mamana Ammiey ta Dan tallafo kaina jikin ta tana cemin nayi shiru muka dauka hanya, bansan min bar Ringim ba hold up da muka fara shiga a Kano yasa na farka na gyara zamana, ta dubeni da murmushi a fuskarta tace " Kin tashi?" Na gyada kaina tareda sake kallon kasa mummy ta rike hannuna se wayatta ta fara ringing, ta Ciro daga handbag ta Kara a kunnen ta tana fadin " Baban Basma bamu karasa ba ma... innanlillahi wa inna ilaihil rajiun! Drug dealing? Ya hayyu ya kayyum! Bari Zan dawo kawai" Na kalleta tana aje wayar nace " Mummy me ya faru?" Tace cikin sanyin murya " Yaya Sa'idu aka kama, Wai Yana drug trading" Seda kaina ya Sara saboda nasan menene a kamaka da drug dealing, nayi shiru Ina tunanin to kenan harda Junaidu in har an Kama Kawu Sa'idu Dan ni na San Yana harkar drugs na taba jin Yana waya Amma ban taba kawowa da Kawu sukeyi ba Kuma ban fadawa kowa ba. Ina jin itada Ammiey suna jajantawa har muka Isa airport Nasha kuka da zata juya Ringim. Nida Rooks da Nads se aunties Dina muka tafi. Dama wasu tun jiya sun wuce Shirin tarbata, shi Honey ne ma bansan inda yake ba tun asuba mukai waya bamu Kara ba. Fadar tayi, ginin kanshi abin kallo ne Haka aka lullube kaina aka Shiga Dani zuwa dakin wadda ta Riki Mama, tana zaune ta manyanta sosae da mutane ko Ina se kamshi ke tashi har seda hancina ya daina jin kamshi. Aka zaunar Dani Akan shimfidar da akai min sannan na saki ajiyar zuciya kowa yare yakeyi se Nads dake gefena take fada min me suke cewa. Aka bude fuskata Suka Gama formalities dinsu sannan Anty Bintu tazo ta tafi Dani dakin maman su Ummiey. Nanma aka Gama sannan aka kaini inda Zan huta, akan gadon na kwanta Rooks na min video lokacin da na yaye fuskata Ina sakin ajiyar zuciya Ina Kuma furta finally. Anan mukai sallah muka ci abinci. Anty Yana ta hada min ruwan wanka tace nayi wanka zaa kaini wajen kakana ya ganni. Nayi wanka na fara amfani da sabulun sannan na fito na samu Amina Abubakar ta fito min da kayan da Anty Falmata ta Bata farin lace ne me manyan flowers ja, dinkin skirt me da riga har na saka riga se gata ta dawo tace na cire ga wasu na saka ta nada min lafayar sannan ta min turare ta Kama hannuna muka fito, Yana tsaye shi da Yaya Hasher. Hannun mu ta hada guri daya tace " Yana jiran ku" Hannuna na janye, tare muka tafi dukkan mu munyi shiru Amma Allah kadai yasan zukatanmu yadda Suka haskaka da farin ciki, har chamber din shi muka je, bayan an Mana iso muka Shiga Yana zaune da yayan shi maza, Wanda ban manta su ba Wanda suka zo tafiya Dani lokacin Abbu na da Rai. Muka tsugunna mukai gaisuwa sannan na dago Jin yace " Yarinyar Halima ta! Allah ya jikanki Halima. Matso kusa dani" Na matsa a hankali ya rike hannuna Yana ta kallona sannan Kuma Yana fada min kyawawan halin uwata da Kuma bani hakurin rashin nemana da sukai. Se ya nuna farin cikin shi da mukai aure sannan Kuma ya Mana nasiha. Bayan nan Suma uncles Dina suka gabatar da kansu sannan Suka Mana tasu nasihar. A wañnan ranar Haka ta Kare a introduction. Washegari very early Ina bacci Ummiey ta shigo tana fadin " Afiyya bacci kike ? Tashi zakuyi missing flight dinku fa" Na mike na zauna nace " Ummiey Ina zamuje Kuma?" Tace " A'a baice Miki zakuje Macau ba? Flight dinku less than three hours fa!" Na gyada kaina I'm going to kill Honey definitely, na ayyana hakan a raina. Na tashi nayi wanka kafin na fito ta fito min da Kaya se lokacin na tuna ya karba passport Dina da yellow card Dina da zai tafi turkey lokacin, Ashe anan ya hada komai. Na karbi tea Nasha sannan na saka Kaya ta Gama saka Amina da Rooks sun tattare kayana, Nads Kuma ta fitar min kayan da already Anty Falmata ta hada min. Dakunan naje nayi musu sallama sannan muka tafi. A mota na Kira Dad da Mom na fada musu zamuje Macau sukace ai sun sani, ita dai seda na Mata korafin an hada Baki da ita, Haka nan mummy ma tace min ai and tafi dasu Kawu Sa'idu Abuja zaa fara Sharia. Presidential suite ne inda akai Mana booking, dama ba wani kulashi nayi ba ko a tafiyar mu saboda fushi nake Yi, shima Yana kulani se kawai ya kyale ni ya saka hannun shi cikin nawa Yana caressing dukda effect din a jikina Amma ban ma kulashi ba. Se da muka karaso sannan na Dan kwantar da kaina akan shi nace " I'm tired" Ya Kara kwantar da kaina akan kafadar shi yace " Your head belongs here!" " Ni ban hakura ba," Yayi dariya yace " To ai nace kiyi hakuri" Muna shiga na aje jakar hannuna sannan ya maida trolley ya aje inda ya kamata ya shige toilet, na kwanta Kan cushion. Ya fito yace " Tashi ki shiga idan kin fito se na Shiga" Na mike na Shiga seda nayi wanka sannan na fito ya shiga, kafin ya fito na shirya cikin bakar riga abaya na duba kibla na tada sallah, yazo yayi tashi kafin ma ya idar tuni bacci ya daukeni ko abinci ba tsaya nema ba I was super tired! Shi ya Nemo abinci sannan ya dawo yazo ya tashe ni, idanuna sunyi jawur har zafi suke min, ya mikar Dani na zauna sannan ya rakani na kuskure bakina ya wanke min fuska sannan muka dawo na zauna ya kawo abinci, shi ya dinga bani inaci seda na koshi sannan yaci. Zan koma na kwanta ya hanani Wai na Bari ya Dan zazzage. After an hour muka kwanta Yana ta shishina wuyana da duk inda hancin shi zai shako, wannan breath din daka fita ya saukar min da kasala na fara tureshi Amma a hankali ya fara rabani da kayan jikina Yana caressing dukkan jikina, blowing me kisses and sucks a Haka muka Raya wannan Daren. Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258. AFIYYA is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258 Conclusion Maimakon mubi jirgin sama zuwa London kawai se yace min why not mubi train ko ferry. Ban taba yin doguwar tafiya a cikin ruwa ba hakan yasa nace kawai mubi ferry. So a kwana da mukai na takwas muka saye ticket aka duba passports dinmu, yellow cards da visas dinmu sannan mukai booking, awanni wajen sama da sha biyar Haka zamuyi tunda flight dinma kusan hakanne. Da sassafe muka fito zuwa can station din, Bayan Gama komai muka dauki hanya se London. Idan muka gaji da Zama se mu fito mu kewaya muga yadda ruwa yake iya ganin ka Babu ko boundary da ya rike ruwan Allah kenan Dhul jalal Wal ikhram. Bamu Isa London din ba se tsakar dare. Kafafuna sun kumbura, idanuna sunyi zuruzuru ga ciwon kai da ciwon Mara. So duk tunani na ko period zanyi tunda leg swelling din ba me yawa bane Kuma nasan nakan Yi hakan duk lokacin da zanyi period. Haka ya dakko kayan da jakata a kafadar shi sannan ya rungumo ni da dayan hannun dukda yayi tambayar duniya nace Masa Babu komai. Ganin Haka yasa ya Mana booking wani daki a cikin motel Dake kusa da station din. Na zauna a gajiye Ina yatsina fuska nace " But honey zamui missing train dinmu fa" Ya zauna gefena yace " Kinganki kuwa? You look terrible kina bukatar hutu. Gobe se mu wuce" Na saki ajiyar zuciya Dan ni kaina bansan ya Zan kasance ba idan har muka ce a wañnan Daren zamu wuce Lancaster. Ruwan wanka ya hada min sannan ya saka na cire kayana mukai wanka shi ne na danji relief Amma ga mamakina se Naga Babu eriod din. Na shirya na kwanta a takure Ina karkada kafata, ya dubeni yace " Afiyya please tell me, me ke Miki ciwo. I'm worried Darl." Na Kama hannun shi cikin nawa nace " Period pain ne, I need a painkiller and pad also" Ya kalleni fuskar shi a hade har ya bude baki zaiyi magana se Kuma ya girgiza Kai ya fita bayan ya bani peck a goshi na. Na lumshe idanuna inajin yadda pains ke radiating jikina. Bai Jima ba se gashi ya dawo hannun shi dauke da Leda, na Mike na zauna ya Miko min tea Nasha sannan ya ballo min painkillers din na afa na Sha da ruwa sannan na koma na kwanta, ya dawo gefena ya zauna a hankali ciwon ya fara karuwa na damke hannun shi cikin nawa, ya shafan kaina ya matso da kanshi kunne na yace " Are you sure ba zamuje asibiti ba?" Na Kara rike hannun shi cikin nawa nace " Zai daina! Just hold me please" Na fada hawaye na gangarowa ta gefen idanuna, cikin sauri ya dauke shi ya durkuso yace " I'm here, we're in together" Se wajen asuba bacci me nauyin ya daukeni, ganin Haka yasa Bai tashe ni ba ya kyaleni shima da ya idar da sallar se ya kwanta mukai bacci har Sha daya sannan na tashi a gigice, nayi bandaki da sauri nayi alwala nazo nayi sallah. Ya fita ya kawo min abinci Dana kalleni a madubi naga duk na rame kamar na Yi kwanaki Ina jinya. Na zauna muka ci sannan mukai wanka muka shirya nayi packing kayan mu danma bamu bude ba. Hudu na yamma muka dauka hanya da daddare muka Isa Lancaster. I felt really at home. Muna Isa seda muka biya gidan su Sheriffa ya karbo key sannan muka tafi. Tun a kofa na fara admiring gidan, ya saka key ya bude na Shiga sannan ya shigo da kayan mu. Kana shiga se siririn corridor anyi painting walls din da favorite colors dina, se shoe rack an jera takalmana da nashi a ciki. Da siririn carpet da zai kaika a parlon Wanda ya hadu da wasu sofas masu kyau. Bai da wani girma Amma ya ishe mu muyi rayuwar wucin gadi. Dakuna biyu ne masu toilet a ciki, se Kuma study room daya da kitchen, ta baya akwai karamin garden da akai shuke shuke masu ban shaawa, kallon gurin kadai is a therapy. Mukai wanka muka shirya sannan yace na Bari zai samo Mana abinci, ni Kuma na kwashe kayan da muka zo dashi na juye cikin built-in wardrobe. Na wuce kitchen na dudduba abubuwa tare da maida su inda ya dace. Ina kitchen din ya dawo muka ci abinci sannan muka fara hira. Cikin aminci da albarka zaman mu ya daure bawai na daina ciwon cikin ba, kullum se nayi Amma se nata daurewa Dan kada na tada Masa hanaklain shi. Ranar da muka cika wata daya da aure na tashi da ciwon kai me tsanani na balla magani nasha sannan naje na kwanta shi a ranar ya fita aiki ni Kuma ban koma school ba. Su mom cikin satin suka dawo dukda Nanny kadai tazo ta ganni. Bayan wani lokaci se bacci ya daukeni akan gado, nayi abuna cikin baccin naji ciwo a cikina kamar a mafarki, nayi ta juyi cikin rashin jin Dadi har na farka, Ina mikewa Dan nufin dakko magani nasha se kawai Naga jini kacakaca akan gadon, na dubi kayan jikina shima duk blood stain dinne. Na yamutsa fuska na ayyana se yau period din ya ga damar zuwa kenan. Na yaye bed spread din na shiga dashi toilet na Dan wanke gurin sannan na jefa cikin washing machine dina, na cire kayan jikina na dauraye sannan na fito. Doorbell naji hakan yasa na kalli agogo sure lokacin dawowar shi yayi, nayi saurin zura riga na tafi bude masa, Yana tsaye da suit dinsa sakale a hannu Yana Jirana, Ina bude Masa ya riko ni tareda fadin " You're sick?" Na gyada Masa kai, ya taimaka min na zauna sannan ya shiga ciki Bai Jima ba se gashi ya dawo ya mikar Dani muka fita se asibiti. Muna zuwa aka karbe mu na fada ma doctor din duk abinda ya sameni, ta kalleni sannan ta danyi rubutu tace akai ni O&G. Muna zuwa aka min scan, sannan aka kwantar Dani ta dubemu ni dashi tace " She was three weeks pregnant!" Da confusion yace " Was?" Ta gyada Kai ta Masa bayanin wannan magungunan da Nasha shi ne ya lalata cikin " I've seen incidences da ciki ke zuwa da ciwon Mara, our ladies usually thinks it's menstrual cramps, they go on with taking anlgesia Wanda in most cases ke harming fetus din. Is same as your case" Ta shafa kaina ganin har na fara kuka, ta furta " I'm sorry, we need to do evacuation, if you ready please do come and sign" Na damke hannun shi inata kuka, wani zafi nake ji dama ciki ne dani nayi ta bankan magani bansani ba. Ya zauna gefena yace " Kiyi shiru kinji, ai Baki sani ba shiyasa. I'm sorry for the pains you've gone through" Ni ko jinshi ba nayi kukana kawai nake Haka ya barni yayi signing sannan suka zo zasuyi min sannan ya fita ya Kira Mom ya fada Mata. Ai kafin a gama ma har ta iso itada Nanny. Suna shigowa ta rungume ni tana fadin " Ya Isa kinji? Kiyi hakuri Allah zai kawo wani" Na share hawayena ta ta tasheni zaune na karba tea nasha sannan ta dinga min nasiha ai ba wani Abu bane ba, I'll still concierge again, Kuma Banga ita ko haihuwar ma Bata taba Yi ba. Maganarta hit my hard, why am I not been grateful? Ita ko conceiving na Bata taba ba balle taji dumin a jikin ta. Na lumshe idanuna bacci ya fara kokarin dauka ta. Kwana biyu nayi na warke sosae aka sallame ni, gida muka fara zuwa a wañnan ranar Dad ya dawo daga Manchester. Ina ganin shi na sake Baki na fara kuka, se ya fara murmushi Yana kallon Yaya Shehu dake tsaye Yana kallona yace " Afiyya ta Zama shgwababiyya! Ya Isa Haka Allah ya Kara sauki kinji?" Na gyada kaina seda mukai lunch sannan muka tafi gidan mu. A mota hannuna cikin nashi yace " Why were you crying? Har yanzun kukan Babyn ne?" Na Kara Bata fuska zanyi kuka yace " Sorry, we will make another baby ko?" Na Dan kwantar da kaina a hannun shi, ya fara murmushi Yana cemin kunyar me nakeji. Na Jima Ina kallon post na Mata a IG Akan complain na sure, yawanci they always complain and spit d bad side of auren, Amma Ina son na fadawa Wanda basuyi aure ba da kada wannan ya tsorata su, kada wannan ya Sagar musu da gwiwa, akwai good stories about aure that are untold. I believe Babu wani Abu da bashi da matsala, ko menene kaui seka samu matsala but ya kamata muna tuna a cikin matsalar akwai Abu me dadi. They said marriage is not all bed of roses and so it's not all bed of thorns! Da farko bamu fadawa kowa ba se dai ya fadawa Yaya Sarki shi Kuma ya fadawa Ummiey, ni Kuma na fadawa Rooks ta fadawa Mummy. Dukkansu seda sukai fadan bamu fada musu ba, da Ummiey zata zo muka ce Mata ai naji sauki seda Dad ya Mata magana sanann ta hakura ta zauna. Na koma makaranta, tun safe na tashi na samu Yana wanka, se na wuce kitchen na hada Masa breakfast Ina Yi Ina gyara gidan har na gama, Ina zuwa daki na samu har ya Gama shiryawa, na riko hannun shi nace " Ina kwana?" Ya langwabar da Kan shi yace " Se yanzun? Kin tafi ko tayani shiryawa bakiyi ba" Na danyi murmushi nace " To ai abinci nake hada maka fa" Ya saki hannuna Yana tayani ninke duvet din sannan muka je yaci abincin Yana tambayata yaushe Zan dawo nace " Se yamma!" Yace lokacin ya gama shima na jiar shi a makaranta. A Haka muka rabu na Gama duk abinda zanyi na tafi school. Two muka shiga lecture dinmu ta karshe a ranar, epidemiology in nursing, ranar zamu fara course din, Ina zaune Ina duba slides din se kawai lecturer ta shigo, da sauri na dago na kalleta Jin murya kamar ta Anty Falmata, na kalleta tare da saurin tashi tsaye, se Naga tana kallona tace " What?" Nayi saurin girgiza kaina na zauna tayi introducing kanta as Zainab Othman, she's Ethiopian Amma tace Mana tana lecturing anan, nayi shiru har ta Gama Ina tunanin yadda zaayi na Mata magana, I remembered ance kakata ta koma Ethiopia da ciki a jikinta, inata kallon ta Ina Kara auna kammannin ta da Yan uwan mama. Har ta fita ko definition din epidemiology din banma Yi picking ba. Tana fita na Mike da jakata mukai sallama dasu Maryam sannan na fito na Isa inda Zan jira shi, nayi shiru very deep in thought Dole ita ce, Yar uwar Mama ce. " Damsel!" Nayi saurin sakin murmushi Ina duban shi ya karaso tare da Mika min hannu, muka gaisa sannan muka dauki hanya, yadda yake min Hira Ina yin shiru yasa ya dinga tambayar ko inada damuwa ne, na girgiza Kai nace Yunwa nakeji. A waje mu kaci abinci sannan muka wuce gida, daki na wuce da kayan mu a hannu na fara lalubo wani tsohon diary din da Abbu ya bani, I remembered reading something similar to wanann. Inata flipping har na samu gurin da ya rubuta sunje Ethiopia shi da Mama, aka ce Mata babarta ta Haifa zainab amma tana UK tayi aure Amma basuda contact dinta. Na rike littafin a hannuna har ya shigo ya karbe yace " Are you ok? Me yake damun ki?" Na zauna na fara fada Masa seda na Gama tas yace " Are you handling this alone? She's my Aunt also. We're in this together" Na saka hannuna Ina zana Masa soothing circles a fuskar shi, hannun ya karbe ya zura a bakin shi wanda yayi sanadin sending wasu waves of vibration cikin jikina, na lumshe idanuna na kwantar da kaina a kirjin shi nace " I love you Darl! Kullum kana sawa Ina jin sonka nake Kara Yi" Ya dube ni da pouted lips yace " So akwai space a zuciyar ki da ban Gama cikewa ba kenan?" Nayi dariya nace " Not at all! Gaba daya cikin zuciyata is filled with you, only you Darl" Baya gajiya da Jin shi din nawa ne, wannan satin ya Kare akan bincike akan Mrs Zainab Othman, se hasashen mu ya tabbatar Dan shi Yana ganinta yace wallahi ita ce. Haka mukai kundunbala muka same ta a office, he clearly explained everything to her, ya Nuna Mata pictures din su Anty Falmata da sauran su, tana ta kallon mu hawayen da am sure hawayen farin ciki ne. Ta hada mu ta rungume mu tace she have waited ko mutum daya yazo nemanta har ta gaji tunda mahaifiyar su tace Mata zasu Neman ta. Haka muka Kira Ummiey muka fada Mata ai a satin se gasu sunzo akai karamin reunion. Na samu sabuwar uwa. Rayuwa ta cigaba da tafiya cikin aminci, kauna da Kuma zaman lafiya, ban Jima ba na samu cikin da nayi ta kukan zubewar wancan, I feel safe ga Mom, Nanny ga Kuma Mamaa kamar yadda nake Kiran Anty zainab. Duk wannan rashin uwar da ake ganin banida shi ta kulle dukkan gaps, a Haka munata turawa cikina ya Kai term Nanny ta dawo wajena, da daddare na fara labor muna zuwa asibiti akace tip of finger, na kalla nurse din nace Mata ciwo nakeji tace eh false labor ne, kamar na daketa Amma Nima na sani a literature. Wasa Wasa seda na Kara sati kafin true labor yazo, anan na ganne tabbas wancan false labor ne. Mukaje asibiti na kusa 12hours Ina Abu daya kafin Allah ysa na haihu yarana biyu. Dukkan su Mata, na saki ajiyar zuciya lokacin da na rike su cikin hannuna, honey Yana sahafa kaina yace " Sannu Darl kinyi kokari" Nayi murmushi Ina kallon su, Ina jin kaunar su har cikin kaina. Mummy sasu Ummiey duka Suka zo lokacin ana Shirin bikin Hafsan Kawu Sa'idu zata auri cousin din su Rooks ta wajen babanta, Nads zata aura Dan Anty Yana Bulama karami, Rooks Kuma bansan yaushe Suka hade da ya Hasher ba se daga baya nake jin labari me dadi, Yaya Sarki Kuma zai aura Amina Abubakar Rogo. Nayi farin cikin wannan Abu. Yara akai suna aka saka Halima da Mariya. Epilogue! Bayan shekara biyar cikin katon prison Dake lagos, Junaidu ne na zaune a wani karamin daki hannun shi dauke da kur'ani da matasa sun taru Yana musu karatu. Wani lokacin mukan Yi tunanin wani hukuncin yayi tsauri not knowing hanyar shiriyar mu ce a hakan, it's a laid down path for us to walk on. Tunda zaa tafi dasu zuwa Lagos da Malam ya same shi ya bashi takaddu ya nuna Masa yayi amfani da damar shi wajen tuba da Kuma kusantar Allah, sannan ya sanshi yayi amfani da abinda ya sani din. Haka yayi kuwa Bai Jima ba ya samu wani dattijo ya nanike Masa kafin shekara ya haddace kur'ani ya Gama littatafi sosae, a shekara ta uku malamin masu ya rasu se kawai ya gaje shi, shi Kan shi idan ya ga Yana huduba a massalaci da yadda ake karrama shi se yayi ta Dana sanin abinda yayi. Kawai Kuma se aka zo anyi lifting sauran shekarun da zaiyi anyi Masa afuwa. A cikin satin zaa sallame shi. Bayan sun Gama karatun ya zauna yayi shiru yana tuna every bit of his life, yayi sujadda ta godiya sannan ya dauki niyyar daurawa daga inda ya tsaya, ba zai cigaba da Bata rayuwar shi Akan duniya ba!!! Cikin lokaci na Gama karatuna na Zama kwararriyar Nurse me licence to practice, yarana sun girma har na Kara samun wani cikin na Haifa Abbu na. Duk abinda na kalla se naji ya wuce, nasan Nasha wahala Amma yanzun na manta no ce wannan yarinyar a gidan Kawu Sa'idu da tayi bauta kamar baiwa a lokacin da, wadda aka Mata aure da Wanda Bata sani ba, na shafa fuskata da Banda kyallu Babu abinda take, na tuna Mari da nasha kala kala akai, na dubi masoyi na, farin ciki na nutiswata Yana koyawa Hisham rubutu yayinda Ayaan ke rubutu cikin karamin littafi se hairan a makale a jikina, sune farin ciki na su dinne rayuwata. Kowacce da take ganin rayuwa ba zata daidai I'm gonna tell you that at the end of tunnels there's light! There goes my hands shaking You're the reason My heart keeps beating I need you now! If I can turn back the clock Make sure the light defeated the dark I'll spend every hour of every day Keeping you safe! I climbed every mountain Swim every ocean Just to be with you Fix what a broken Cuz you need to see that you're the reason! Alhamdulillah!!! AFIYYA is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of Nigeria. Send evidence of payment to 09063467258.