FAHIMAH Book 1 Complete Writing by Takori kabara arewanovels.com.ng SHIMFIDA Misalin karfe ukku na yammacin ranar, wadda ta kasance Talata, cikin wata Unguwa a jihar Kano da ake kira ''Yankaba, Hajiya SAFIYYAH-BASUDANIYYAH (kamar yadda kowa da ya santa yake kuma alaqa da ita ke kiranta), na zaune bisa Kilishin tsakiyar falon ta, carbi ne dan madina a hannun ta tana ja, lokaci zuwa lokaci tana mai daga kanta zuwa ga tankareren agogon bango dake manne a fuskar gabas maso kudu na falon nata. Ga dukkan alamu akwai abinda take dakon jira, shiyasa tun da ta yi sallahr azuhur bata tashi a gurin ba take yawan kai idanun ta ga agogon bangon. Kayataccen falo ne ne da ya ji kayan alatu na zamani wanda kallo daya zaka yi masa ka tabbatar masu gidan suna cikin wadatar rayuwa, daular duniya ta gama zaunawa dai-dai misali da burin kowanne dan adam. Komai dake falon kalarsa ruwan madara ne da ratsin ruwan goro (orange) wanda hakan ya maida falon kalar unique don kala ce da ba'a faya amfani da ita ba wajen tsara falukan zamani. Tun Haj. Safeeyah bata damuwa, amma da ta ga yadda lokaci ya ja sai damuwa ta fara nunawa akan kyakkyawar Basudaniyar fuskar ta. Me ya tsayar da FAHIMAH a makaranta har yanzu da ake neman karfe uku na rana??? Sallamar mai aikin ta Talatu ya katse mata tunani, ta shigo dauke da butar Shayi irin ta larabawan SUDAN da 'yan kananan kofunan tangaran na shan shayin Sudanai, kai tsaye ta nufo inda uwargijiyar ta ke zaune ta russuna daga gefe ta ajiye, ga dukkan alamu abu ne da ya zamewa Hajiyar al'ada wato shan shayin akai-akai. Talatu tace, tana duban Hajiyar. "Hajiya mutuniyata ko lafiya? Tun dazu nake duban hanyar ta har yanzu shiru, ko ta ce miki zata biya wani waje ne yau?" Hajiya Safeeyah ta kai karshe a carbin da ta ke ja, tayi addua suka shafa tare da Talatu, sannan ta ce. "Tunanin da nake ta yi tun dazu kenan, karfe daya da rabi yau tace min zata dawo, bari in kira wayar ta mu ji ko lafiya, don Fahimah bata zuwa wani waje ba tare da ta gaya min na mata izni ba". Ta dauki wayar dake gefenta ta lalubo lambar Fahimah ta kira ta kara a kunnen ta, amma har tayi ta katse mai wayar bata amsa ba. Which was very unusual of her (kin daga waya). Wanda hakan ya kara dugunzuma zukatan Hajiya da Talatu. Daidai lokacin da ya shigo falon yana balle 'links' din hannun farar rigar shi, gabadaya falon ya dauki kamshin sassanyan turarensa "Maison Francis (Kurkdjian, Paris)". Farar shaddah ce kal a jikin shi mai santsi da ake kira (London King) da farar hular Zanna mahadin shaddar jikin shi. Dogo ne, mai fadin kirji (physique chest) amma hakan bai hana ka kira shi siriri, don tsayi har ya rankwafa, kallo daya zaka yi mishi ka tabbatar ba cikakken bahaushe bane; ko dai ruwa-biyu (half-caste) ko kuma cikakken Ba-sudane. Sudanan ma irin fararen Sudanai ba bakaken cikin su ba, hancinsa don tsayi har lankwasawa yayi kadan, hular kansa ta nitse tsaf a cikin tarin sumar kansa wadda ta kara fallasa jinsin da ya fito daga cikin sa. Ga dukkan alamu cikin sauri ya ke, sauri mai yawa, ya dubi mahaifiyar sa dake zaune nannade cikin laffaya shudiya da carbi a hannun ta, bai taba ganin ta da wata suttura ba ta Sudanese ba, Talatu na duke gabanta tana firfita mata shayi, yayi dan russunawa daga tsaye cikin tarin ladabi ga mahaifiyar sa... "Ammi zan fita, zan koma office, don bamu tashi ba na dawo, amma bazan wuce karfe biyar na yamma ba yau zan dawo, insha Allah. Na baro wasu ayyuka da ban karasa ba nake so inje in karasa, don gobe da safe managern Gyadi-gyadi Branch zai karbe su daga ofis dina". Bai kuma jira cewar mahaifiyar tasa ba ya doshi kofa, ko abincin ranar da aka shirya masa bisa makeken tebir din falon bai kalla ba. "Uwais!" Muryar mahaifiyar tasa ta dakatar da shi. Ba tare da ya juyo ba ya dakata a kagare. Ta ce, Fahima ba ta dawo ba tun fitarta makaranta. Annurin da ke fuskarsa nan da nan ya gushe. Gabadaya ya juyo fuskarsa a gintse, For Allah sake. Ammi ni ina ruwana? Is she a kid? Ko kuwa ba ta san hanya ba? Hajiya Safiyya ta girgiza kai tana iya karantar tsanar maganar yarinyar da ta yi masa baro-baro a kan kykkyawar fuskarsa. To amma dole ta gaya masa sabida yadda kasar tamu ta koma daukan dan mutum ya zama kamar na kiyashi. Babu kuma wani namiji a gidan bayan shi, shi ne ubansu har ita da ta ke mahaifiyarsa. Duk uzurin da ka ke da shi ka ajiye ka bi bayanta, ko in tashi ni da kaina in bi ta. A matukar fusace ya sa kai ya fita daga falon ba tare da ya ce komai ba. Daga yadda yake tukin motar kadai za ka fahimci ransa a bace yake, don dai fuskar sa ta kasance mai boye bacin rai ne, ko kadan ba abin da ya tsana a duniya irin Ammi ta hada sha'anin sa da na Fahimah. Ta ki yarda ta gane har yau shi zuciyarsa ba ta son Faheemah, kuma har abada ba za ta so ta ba! Ba don komai ba sai don ASALINTA.... Da wasu specific dalilan da suka dade da samun muhalli a ransa tun suna yara shi da Fahimar, muhimmi shi ne son da Ammin sa ke mata, wanda yake ittikafin da kyar in bai zarce wanda take masa shi da ta haifa ba. Shi kuma tun asali mutum ne mai kishi akan abinda yake so, musamman Amminsa, wanda kishin nasa akan ta ne ya hanata sake aure har yau. A daidai lokacin ya karya kan motarsa ya shiga makarantar YAN DUTSE COLLEGE, bayan maigadi ya bude masa kofar makarantar, abin haushi yana shigowa ita ya fara hangowa tun daga nesa suna tafe ita da kawarta Majida suna hira, sai dariya ta ke ba abinda ya dameta. Ta baro masa uwa cikin taraddadi don bata san zafinta ba. Her elegant black skin sai sheki ta ke cikin hasken ranar, babu wani abu mai haske a jikinta kamar fararen idanunta da jerarrun hakoranta. She's dark-skinned yet beautiful. Wasu irin idanuwa masu sparkling cikin idanun duk mai dubanta. Cikakken gashin girar da ya kusa hadewa da dan uwansa yana daga cikin abin da ya bambanta ta da sauran mata yan uwanta. Uwais dauke kai ya yi yana sakin tsaki, tare da danna musu gigitaccen horn mai karfi don kamar ba su lura da tsayuwar shi ba. A ransa cewa ya ke, ko uban me suka zauna yi a makarantar har yanzu oho! Kwata-kwata su da suka rage cikin makarantar ba su fi a kirga da yatsun hannu ba. Ta dago kai da sauri ta dubi inda horn din motar ya fito. Mutum na karshe da ba ta taba tsammanin gani a makarantarsu ba, da sunan dai ya zo daukanta. A gurguje ta yi sallama da kawar tata ta nufo inda yake kafafunta har hardewa suke don sauri da fargaba. Ba yau ta fara ganin wannan moody expression din a kan kyakkyawar fuskarsa ba in dai a kanta ne, don haka inda sabo Fahimah ta saba. Ta bude kofar gefensa ta shiga, ya tada motar a guje ya bar makarantar ba tare da ya dube ta ba. Maimakon ya dau hanyar gidansu kamar yadda ta yi tsammani, sai gani ta yi sun dau hanyar Bank Road, ita dai ba ta ce komai ba, amma ganin sun yi parking a wani branch bankin GT ta fahimci inda suka zo din, wajen aikinsa ne. Ya bude kofarsa tare da daukar jakar loptop dinsa da wayoyinsa ya yi shigewarsa. Duk inda ya gifta sai maaikata yan uwansa sun kula shi sun gaishe shi, amma hannu kawai Uwais yake daga musu ya wuce, kowa ya saba da rashin walwalarsa shi ya sa shan kamshinsa ba ya damun kowa don farin jini gare shi ba na wasa ba, wanda kyawun surarsa ke sayo masa. Yana kokarin zama a kujerar ofishinsa wanda ke zagaye cikin raw gilashi, kowa da ke wajen yana iya hango shi daga waje, wayar Ammi ta shigo, yana jan kujerarshi zai zauna ya amsa mata. Muna tare. Kawai ya ce tare da ajiye wayar bisa makeken tebirinsa baki wuluk mai sheki. Ammi hankalinta ya kwanta tunda ya ce yana tare da Fahimar. Kai ba za ka ce ya ajiye mutum cikin mota ba, ya kunna kwamfutar kan tebirinsa ya durfafi ayyukan da ke gabansa cikin kwarewa da sanin makamar aikin sa, wadanda da ma su ya dawo don yayi. Ya manta da wata da wata mutum dan adam da ya ajiye a cikin mota, ba tare da ko ya sauke mata gilashi don ta sha iska ba. A can kuma Faheema tun tana duba siririn agogon da ke daure a hannunta har ta kwantar da kanta a kan dash board din motar, ta sauke gilassan da ya rufe iska ta soma ratsa ta, wata irin yunwa na sakadarta. Rabonta da abinci tun karin kumallon safe da Ammi ta takura mata ta yi, ta san halin Uwais sarai, duk yadda aka yi Ammi ce ta takura masa ya bi sawunta shi ya sa ya zo ya shanya ta a harabar ofishinsu. Ba kowa ya ja mata ba sai Mr. Edward malaminsu na Biology, shi ne ya zaunar da su yin practical na darasin da yake daukarsu bayan normal school hours kasancewar nan da watanni uku za su zana jarrabawar barin makarantar sakandire gabadaya. Ammi ta san Uwais ba ya son hada hanya da ita don me za ta sa shi ya biyo bayanta?! Allah sarki Fahimah! Tun tana sauraron kidan da akuyar cikinta ke yi, har ta koma ta kwantar da kanta jikin kujerar motar, wani wahalallen barci ya yi awon gaba da ita. Sai karfe biyar na yamma ya kammala duk abin da yake yi a bankin, ya tattaro wayoyinsa da kwamfutarsa ya fito. Sai da ya tunkaro motar sannan ya tuna da ita, ya bude gidan baya ya zuba shirginsa sannan ya shiga mazauninsa ya zauna. Kunna motar da ya yi, da reverse hadi da cin taya ya bar harabar bankin shi ya tada Faheemah daga wahalallen barcinta. Barcin yunwa da gajiya. Ta dube shi ta gefen ido, ya nutsu yana tukinsa cikin gwanancewa. "Fuskar ta salihai, kyakkyawa a ido, amma kamar ta Firauna a zuciya. Fahima ta fada a zuciyarta.A shekaru goma shaf takwas na rayuwarta da ta yi tare da shi gida daya, bai taba kyautata mata ko sau daya ba, sannan ba za ta taba iya fadar wani alkhairi guda daya da ya yi mata ba a matsayinsa na Yayanta a kan dalilin da ba ta sani ba. Duk da kasancewar su biyu ne kacal a wajen mahaifiyarsu Hajiya Safiyya, ta sa a ranta Uwais makiyinta ne na babu gaira babu dalili, don bata san laifin da take masa ba, Ammi ma bata sani ba, don har a cikin kwayar idanunsa tana iya hango tsantsar kiyayyar da yake mata, a gaban kowa kuma ba ya iya boyewa including mahaifiyarsu Ammi Safiyyah. Ita kuma nan duniya babu mai burge ta irin UWAIS ABDULKARIM SHAGARI!!! Wani kwayan mutum guda daya da ya yi mata babakere a zuciya.Daga baya ta fahimci shi Ammi ta haifa ba ita ba daga lokacin da ta soma hankali, amma in za a yanka ta ba ta san alakar da ke tsakaninta da su ba. Ita dai ta taso ta ganta a gaban Hajiya Safiyyah Basudaniyyah, cikin wata irin kulawa irin ta UWA da duk wata kyautatawa da uwa ke wa danta. Ammi Safiyya is more than a mother a gare ta, she is an ANGEL wadda Allah ya halicce ta a hannunta domin ta zame mata kafadar da za ta kwanta a kai ta yi kuka, ko dariya. Yawan kyautatawar Ammi, jin kai da kulawarta gare ta ke hana ta yi mata titsiyen da Ammin ba ta so na ita wace ce uwarta, wane ne ubanta??? In tana son ganin bacin ran Ammi, to ta yi mata wadannan tambayoyin. Don haka ta dade da daina yi mata tun kafin ta kawo munzalin adolscence. Ta yarda da abin da Ammin ke gaya mata kullum, ITA CE UWARTA, ITA CE UBANTA amma ta sani watarana na zuwa da dole Ammin za ta yi mata confessing daga inda ta samar da ita tunda ko makaho ya shafa a halitta ya san Ammi balarabiyar usuli haka ba ita ta tsugunna ta haife ta ba. Kodayake ba'a judging haihuwa da kamanni ko kalar fata, amma ita kam ko daga kalar fata, gashin kai da yanayin kirar jiki za ka san Ammi balarabiya ce, yayin da ita kallo daya za ka yi mata ka tabbatar cikakkiyar bahaushiya ce, jikar Barbushe da Tsimbirbira. To amma me ta ke nema a iyaye wanda Ammi ba ta yi mata ba? Ta yi mata komai a rayuwa wanda a kullum yake mantar da ita cewa, ba ita ta haife ta ba, sai dai kulafuci irin na dan adam. Musamman akan son tabbatar da legitimacy din ta. A duk lokacin da wani tunani makamancin haka ya sarke ta, fuskar Ammi da murmushinta na UWA a gare ta take daukowa ta dora a kan idanunta, sai kowanne tunani, da kowacce damuwa da kowanne bacin rai su bace su kama gabansu. A duk lokacin da Uwais ya yi mata kallon nan nasa na tsana da kyama, murmushin Ammi kadai ke gusar da shi komai girmansa. A yayin da ka ke da uwa irin Ammi a gefe, babu wani bacin rai a rayuwa da ya isa ka yi masa kuka. Fahimah ta kan yawaita fadar hakan a zuciyarta. Tana wannan tunanin cikinta kuma na ci gaba da kartawa ta ji Uwais ya kashe motar a parking lot na gidan su, sai a lokacin ta ankara sun zo gida. Ya fice ya barta a motar ba tare da ya ce da ita ko uffan ba. Tana fitowa jiri ya kwashe ta, sai da dafa bango sannan ta iya karasawa zuwa cikin gida. Shi tuni ya jima da shigewa part dinsa. Wanda dole sai ka ratsa ta main parlour zaka isa part din nasa. Ammi bata yarda ta ware shi daga can waje ba, sabida tsantseni na tarbiyyah irin nata. Ammi da Talatu har suna hada baki wajen tambayarta lokacin da ta shigo wujiga-wujiga da ita. Fahimah, me ya zaunar da ke a makaranta haka? A gurguje ta yi musu bayani Mr. Edward ya tsare su kan shirye-shiryen su na fara SSCE, da sassanyar muryar ta wadda ta kara sirancewa sabida yunwa da gajiya, sannan ta durfafi dining-table tana zuba abincin jikinta har rawa yake, kuma da ma tana da ulcer. 9/23/21, 8:15 PM - Buhainat: A bakin get ya tadda Jabir yana jiransa, a motar Uwais za su tafi, in sun dawo ya ajiye shi a gidansa ya juya. Tunda suka hau kan titin da zai kai su Bompai wuta ta dauke wa Uwais saboda fargabar irin tarbar da kuma amsar da zai samu daga Alhaji Umar Dikko. Jabir shi kadai yake zuba hirarsa ga dukkan alamu shi kam bai da sauran matsala a rayuwa, da ya fahimci halin da Uwais ke ciki, sai ya yi dariya ya dafa kafadarsa. “Daddy is very friendly, kawai za ka sha tambayoyi, in ya ga dama kuma ya ce ka jira auta for 6 years ta gama MBBS dinta. This is for sure na tabbata zai fadi hakan. Ashe da na tattaro kayana na koma gidansa a Abuja idan yana ganina kullum zai gane ba zan iya jiran ba". Dariya Jabir ya sake yi, ya ce, Kada ka tsorata da dukkan tambayoyinsa, be brave, be yourself, sannan kada ka boye masa komai ya tambaye ka. Alhaji Umar Dikko na zaune a luntsumemiyar kujerar sitting room dinsa, da ganinsa ka ga bafillacen usli, furfura ta cika a gashin kansa amma fatar jikinsa sumul ta ke, babu tsufan, sabida samun hutu. Jabir ya yi musu iso suka shiga already ya san da zuwan nasu. Dukkansu a kasa suka zube suka kwashi gaisuwa, irin ta neman iri, fuska sake yake amsawa har yana tsokanar Uwais ya aka yi ya bari abokinsa ya shiga daga ciki shi yana daga waje har yanzu? This is kafin ya ji gundarin abin da ke tafe da su. Daddy, kamar yadda ka sani Uwais abokina ne, tun a A.B.U, Daddy abin da ya kawo mu shi ne, ya zo neman amincewarka ya fara neman auren Amrah. Cikin mamaki Alhaji Umar Dikko ya ce, Amrah? Amrah wacce? Jabir ya ce, Autar Mama dai Daddy. Ya tsura wa Uwais ido na 'yan dakikai inda ya hango cikar kamalarsa ko ta ina bai ga makusa ba kamar yadda komai da ke jikinshi ya nuna ba karamin mutum ba ne, ilmi da hatimin nasara sun wadace shi. Sannan ga wani irin sassanyan kyau da ya rasa gane daga kabilar da ya dauko shi. Above all Allah ya yi ma Uwais wani irin kwarjini, ilhama da cikar zati da ya wuce ya nemi alfarma wurin mutum a kasa yi mass. Amsar da ya so bayarwa sai ta canza kanta ba tare da ya ankara ba, domin da farko so ya yi ya ce su tashi su tafi, ba yanzu zai yi wa yarsa aure ba. Wane ne Babanka? Kai dan wace kabila ne? Gama na ga ba Bahaushe bane Uwais ya muskuta sannan ya kara dukar da kansa in ka ganshi a wannan lokacin kamar bawan da ke neman taimako. Ji yake zai jure komai, zai iya komai in dai Alhaji Dikko zai ba shi auren Amrah a karshe. "Sunanan Babana Grand Khadi Abdulkarim Shagari, ya jima da rasuwa, na girma a hannun mahaifiya ta, Babana basakkwace ne, mahaifiyata basudaniya ce. Alhaji Dikko ya gyada kai, sannan ya kara jifansa da tambaya. Mene ne matakin karatunka? Kuma mece ce sanaarka? Uwais ya zuki numfashi, a ransa ya ce, wannan wane irin mutum ne? Ina da kwalin digiri na biyu, sannan ni banker ne da Guaranteed Trust. Alhaji Umar Dikko ya gyada kai cikin gamsuwa, sannan ya ce, Kana da masaniyar cewar Amrah karatun likita ta ke yi a matakin farko? Za ka iya jiranta ta kammala tsawon shekaru shidda? Uwais ya hadiyi yawu da kyar shi fa jiran ne ba zai iya ba, burinsa ya bude ido ya ga ya mallaki Amrah, don haka bai yi kasa a gwiwa ba. Daddy, ku yi min alfarma, na yi alkawarin barin Amrah ta yi ta karatunta a dakina har sai ta ce ya ishe ta. Ya kara dukar da kansa cike da zullumi da fargabar amsar da zai samu daga Alhaji Umsr Dikko. Bai san dalilin da ya sa farad daya yaron ya shiga ransa ba. Kamalarsa ce ko kamewarsa? Ba zai iya cewa ba, ga wasu exceptional qualities da ya gani a tare da shi. Shi kansa Jabir a yadda ya san mahaifin su bai zaci tambayoyin Daddyn nasu za su tsaya a nan ba. Sosai Alh. Umar ya dubi Uwais kafin ya ce, Na ba ka izni ka nemi auren yata. Idan ta amince da kai dari bisa dari zan iya ba ka aurenta a bisa alkawarin da ka yi min na cewa za ka barta ta ci gaba da karatu a gidanka. Besides ni kuma zan yi nawa kyakkyawan binciken a kanka da iyayenka, idan na samu wani mummunan hali a tare da kai zan dakatar da kai. My daughter is innocent ka yi taka tsaftacciyar muamala da ita a cikin neman aurenta. Farin ciki ya sa bakin Uwais ya kasa rufuwa, kansa a kasa ya yi godiya tare da alkawarta wa Daddyn insha Allahu zai kiyaye abin da ya fada masa, kuma da yardar Allah ba zai samu wata mummunar shaida a kansa ko iyayensa ba. Suka fito shi da Jabir, inda Jabir din ya ja shi suka shiga cikin gidan wajen amaryar Babansu Aunty Nana. Suka gaisa tana da kirki sosai. Jabir ya gabatar mata da Uwais matsayin abokinsa, kuma manemin auren Amrah, wanda Daddy ya san da zamansa a yanzu. Aunty Nana ta yi mamaki sosai, don ta san Daddyn ya ce ba zai aurar da Amrah ba sai ta kammala MBBS. Ta karbi Uwais hannu bibbiyu, ta yaba da komai nasa cikin ranta. In Amrah ta same shi, to hakika ta yi dace da miji na nuna wa saa. Suka taho gidan Jabir inda Uwais ya sauke shi, Jabir ya yi masa tayin shiga gidan ko zai so yin magana da Amrah. Uwais ya yi murmushi ya ce da shi, Not now, Im not in contentment, tunda na samu licence dina. Zuwan Uwais na farko wajen Amrah a wani daren asabar ne, ana tsula ruwan sama, ruwan har ya fara jika shi, a lokacin da ya yi parking ya fito daga mota, ya bi ta garage zuwa falon Jabir inda nan ne ba shi da shamaki, kuma sun yi waya da Jabir ya ce yana gida ita ma Amran tana nan. Amma ya ce masa ya zo da wuri don Amrah in ta fara karatun darenta ba ta so a katse ta. Kuma wannan ne karo na farko da za su ga juna officially, ta sanshi a fuska amma a matsayin abokin Yayanta. Yana zaune a falon Jabir yana mai duba agogon hannunsa. Jabir ya ce da shi ya jirata tana zuwa, sannan ya gaya wa Murjanatu Amrah na da bako a falo, kuma da sanin Daddy ya zo ganinta. Bako daga Daddy? Amrah ta tambayi Aunty Murjanatu cikin mamaki. Murja ta ce, Haka dai ya ce, kuma ki yi sauri yana jiranki. Ko kadan Murjanatu ba ta yi mamaki da zuwan Uwais yau wajen Amrah ba, don ta dade da sa wa a ranta in ka ga kare na sunsunar takalmi dauka zai yi. Amrah ta yi sallama a falon da siririyar muryarta mai kidima nutsuwar Uwais. Mikewa tsaye ya yi ba tare da ya san lokacin da ya yi hakan ba. Har sai da Amrah ta shigo suka tsaya suna kallon-kallo ta hasken farin kwan lantarkin da ke falon. Zuciyarsu na bugu iri guda a lokaci guda, yayin da Amrah ta ji tamkar an sauke mata wani nannauyan dutse daga kirjinta. Uwaisun da ta ke kwana da shi tana tashi da shi Uwaisun da ya yi wa zuciyarta babakere ya hana ta sukuni da jin dadin rayuwar ko ta ya ya, yau ga shi a gabanta officially ya kawo kansa matsayin manemin auren ta..Me zata ce? Ko me zata yi? Banda tazbihi ga Ubangiji? Ita ta fara dauke idonta daga cikin na Uwais amma ta yi-ta yi ta furta kalmar ina wuni? Ko sannu da zuwa ta kasa. Zama ta yi a kujera mafi kusa da ita, ta jingina kanta a makarin kujerar don hana kafafun ta kayar da ita daga wadannan kaifafan sexy eyes din na Uwais, tana sauke numfashi a hankalitamkar Uwais ya karanci abinda ke ranta, sai bai wahalar da kansa wajen gabatar da kan sa ba. Kai tsaye ya tafi straight to the point . Amrah am I welcome as a husband? Uwais ya fada daga karshe, yana mai durkusawa a gabanta a kan gwiwoyinsa.... wani abu abu da bai taba tunanin zai iya yi a kan diya mace ba. Murmushin da Amrah ta yi, da fuskarta da ta rufe da tafukan hannunta kadai a matsayin ta na bafullatana tamkar amsa ce ga UwaisUwais Shagari, Uwais Abdulkarim Shagari.... and that is the beginning mafari, tushe, sila, na dukkan abubuwan da suka biyo baya......Sannan silar data zamo hanyar auren UWAIS da FAHIMAH...... **** Ya dauki lokaci mai tsayi yana zuwa zance wajen Amrah, sun fahimci juna sun yarda da juna, soyayya ta yi kaka-gida, hutun nata da ma na watanni uku ne, har ga shi gobe za ta koma Abuja inda daga can za ta zarce makarantarsu ta Limkwokwing, Malaysia. Yau da ya zo sallama ce za su yi, in ka gansu very emotional kamar masu shirin barin duniya don damuwa, Amrah ta shiga ran Uwais yadda ba'a zato haka Uwais ya samu matsayi mai girma a zuciyar Amrah, ta yadda suke jin rabuwar tasu ta yau har cikin bargonsu. Ba don kada in yi wa Daddy laifi ba ya ce zan hana ki karatu, da na kawo miki ziyara a Malaysia. Amrah ta zaro ido ta ce, Kada ma ka fara 'Habib - Qalby', Daddy bai hada karatu na da komai, za mu kasance a waya koyaushe insha Allah. Abinda zan sake dawowa bayan watanni hudu kuma a nan Kano zan sake yin hutuna?. Ke kike ganin watanni hudu kwana hudu Amrah, i see them like eternity. To Amrah ta ya ya zan amince ni ina nan goho ina jira, wani a can ba zai min shigar sojan badakkare ba?. Ya fada sounding emotionally worried. Amrah ta yi murmushi, ta ce, Tunda Daddy ya amsa maka, to ka kwantar da hankalinka ya tsumma a randa, domin Daddy ba ya magana biyu. Sannan ni wa zan kula? Karatun da ke gabana kadai ya ishe ni, ka yarda da ni Habib-Qalby...(sunan da ta rada masa) a Hausance yana nufin 'masoyin zuciya ta'.. Ya ce, Na yarda da ke Amrah, in na ce yarda ina nufin yarda ta har abada cikin aminci. Ki yi karatu mai yawa with me in mind and our next coming babies. Amrah ta kai tafukanta ta rufe fuskarta cikin jin kunya. Ba ta ga lokacin da Uwais ya taso daga kujerarsa ba, sai tsinkayarsa ta yi tsaye a gabanta, hannayensa duka biyu zube cikin aljihu, ya ce, Amrah kin amince min kafin ki dawo in tura magabatana wajen Daddy su kara rokonsa a gabatar da neman aurenmu? Na yi alkawarin za ki cigaba da karatunki ko da kina Malaysia ni ina nan Kano. And I promised you eternal love Amrah, jiran ne ba zan iya ba. Amrah ta kai hannu ta rufe fuskarta, kyakkyawan murmushin da ke kan fuskarta kadai amsa ce ga Uwais, na ta amince ya tura neman auren ta. Don haka da karfin gwiwarsa ya koma gida duk da yana cikin alhinin rashin Amrah da zai yi a kwanakin. Ta riga ta zama wani bangare na ruhinsa cikin dan lokaci kalilan. Ya shigo gida misalin karfe goma na dare. Tuni Ammi ta dade da kwanciya. Har ya shiga bangarensa. Ya yi wanka ya canza kaya zuwa Pajamas farare sol ya ankara da yana jin yunwa, yunwa sosai da ke bukatar tallafi, ya san yanzu Talatu ta jima da komawa Baskwata, Ammi kuma ta kwanta, don haka ya yanke shawarar zuwa kitchen ya nema wa kansa dan abin da zai iya ci ko ya yi barci cikin nutsuwa. Ta juya baya tana fasa kwai a cikin tangaran, ita ma yunwar daren ce ta taso ta, kawai sai ta jiyo takun mutum a bayanta, ta juyo da sauri duk da kamshin turarensa ya riga ya gaya mata ko waye. Ya sunkuya ya bude firji ba tare da ya lura da tsayuwarta ba, Fahima ba ta kara mallakar kanta ba daga lokacin sabida rudewa da bugun zuciya wanda ke faruwa da ita a duk sanda ta ga Uwais. Kwan hannunta ya subuce ya fashe a kan kafarta, daidai lokacin da ya dago da gorar ruwa a hannunsa sai idonsa cikin na Fahimah. Wani haushi ya kama shi da karfi ya ce, What are you doing here? You Goddam Black, mai idanu irin na kyanwa! Ganinki cikin dare sai ya firgita mutum get out from here. Ya fada da tsawa. Jikin Fahimah na mugun rawa ta juya ta bar kicin din, ko kamin ta kai dakinta hawaye ya jika fuskarta. Ta tsani tsawa, ta tsani kyara da hantara. Amma inda sabo ya kamata a ce ta saba da su daga bakin Yaya Uwais, don tun tana karama duk wata haduwa da za su yi in dai ba'a gaban Ammi ba ne to irin haka ce ta ke kasancewa. You goddam black Ta saba da wannan kalmar. Shin laifi ne in mace ta kasance baka? Shin kyawun halitta shi ne yake sa wa a so mutum? Ko kuwa dai akwai wani dalili da ya sa Uwais ya tsane ta bayan wannan da rashin asalin ta? Za ta so wani makusancin sa ya samo mata wannan amsar daga Yayanta Uwais. Amma ta san ba za ta taba samun wannan alfarmar ba, ta sanin wani abu da ya danganci wannan kwayan mutum guda daya mafi soyuwa a zuciyarta, sannan mafi munana mata. Yunwar da ya shiga kicin din da ita sai ya ji ta dauke sabida bacin ran ganin Fahima. Tsaki ya yi ya ajiye gorar ruwan ya koma daki. Ya yi nafilfilin da yake yi kafin ya kwanta sannan ya dauko waya ya kira Amrah don jin muryarta ne kadai zai sa ya yi barci lafiya. Sun dade suna hira, planning iri-iri na irin yadda za su gudanar da rayuwar aurensu. Hatta yayan da za su haifa sai da suka kayyade. Sannan suka koma musun da wa suke so yayan su yi kama, shi kuma ya dage da ita yake so su yi kama itama ta dage da shi take so, a haka suka shiririce suka bata lokaci. Hirar da ta kai su har sha biyun dare, sai da Amrah ta soma hamma sannan suka yi sallama. Da wani irin nishadi Uwais ya yi barci don in yana gaban Amrah ko yana jin sassanyar muryarta manta kansa yake yi, duk wannan miskilancin da izzar nemansu yake ya rasa in dai yana tareda Amrah, in ka ji shi yana zubo hira da kalaman soyayya ka kuma sanshi a tsumammen Uwais dinsa manajan GT ba za ka taba yarda cewa shi ne ba. Fahimah a wannan dare ba ta runtsa ba. Ba bacin ran abin da ya yi mata ke damunta ba, aa soyayya ce ta ke nukurkusarta, soyayyah yar usli mara algus daga indallahi wadda ba za ta iya tantance daga lokacin da ta samu muhalli a zuciyarta ba. Abin da ta sani kawai shi ne, ta taso cikin son Yaya Uwais ba tare da ta san hakikanin mene ne maanar feelings dinta a kansa ba. Sai yanzu a hankali da hankali ya soma game jikinta, ta fahimci zuciyarta is infactuated sosai a kan Yaya Uwais, son da ta tabbatar ba zai taba amfana ta da komai ba. Don haka a wannan dare Fahimah ta yanke shawarar fara adduar Allah ya cire mata Uwais daga zuciyarta ko ta samu sa'idah. Ya munana shi a zuciyarta kamar yadda ta ke mummuna a tashi zuciyar. Har aka yi kiran assalatu ba ta yi barci ba, tana kai wa Sarki Allah kukanta a kan Uwais. Amma ko da ta kwanta barci bayan ta sallaci asubahi, mafarkin da ta yi ya firgitata... 9/23/21, 8:15 PM - Buhainat: ***** Washegari da ta gama shirinta tsaf na tafiya makaranta ta cimma Ammi a dakinta tana karatun littafin Bulugul Maram da ta ke yi duk safiya. Ta tsugunna a gabanta ta gaishe ta sannan ta yi shiru tana wasa da yatsun hannunta. Ammin ta lura akwai magana a bakinta, ta rufe littafin ta ce, Ya aka yi autar Ammi? Kina son wani abu ne? A hankali Fahimah ta motsa dan bakinta kamar mai tsoron abin da za ta fada. A karshe ta daure ta ce, Ammi don Allah kada ki ce Yaya Uwais ya dauko ni a makaranta, don yau ma muna da practical na food and nutrition. Ammi zan dawo da kaina tunda gobe Surajo (direbanta) zai dawo. Ammi yar ki ta girma, ki bar ta ta dinga yin komai da kanta. Ta karasa da murmushi. Murmushi mai sauti Hajiya Safiyyah ta yi, alkunyar yarinyar na sa wa ta kara shiga ranta. Ta tabbata Uwais rashin kirkinsa ya yi mata jiya, sannan ya hora ta da ynwa, amma ba za ta fada mata kai tsaye ba sabida kawaici irin nata. Ta kai hannu ta shafa kan Fahimah affectionately.. I will not send him to pick you again, na lura da yadda ya azabtar da ke da yunwa jiya, amma kansa ya yi wa. Ungo kudin mota ki hawo adaidaita ki dawo gida. Ta karbi kudin da hannu biyu ta yiwa Ammi godiya ta wuce. Ammi, sai na dawo!. Ammi ta ce, Rehlah Saeedah (wato a dawo lafiya). Bayan wucewar yarinyar Hajiya Safiyyah ta lumshe ido ta jingina bayanta da bango tana tunani. Anya mafarkin ta zai zama gaskiya? Anya Uwais zai cika mata burinta? Idan kuma ta tursasa shi anya tirsasawar za ta haifar da Da mai ido? A kafiya da miskilanci gami da izza irin nasa da ta dade da sani? To in ba shi din ba wa zai auri Fahimah ya rike mata ita da amana? "Babu!" Amsar ta kutso da karfi cikin kwanyar ta. Ko ta samu masoyi ya ji ko wace ce ita guduwa zai yi, in kuma ya karbe ta a haka tofa babu daraja da martaba. Uwaisun dai da ta haifa shi kadai ne guarantee dinta a kan Fahima, amma baro-baro ya nuna gara kowa da shi in dai a kan ya so Fahimah ne. son ma irin wanda ita ta ke mafarkin ya yi mata, wanda ya kasa karbarta a kanwa ta jini, ta ya ya zai yarda ya karbe ta a matsayin MATARSA? Shekaru goma sha biyar a baya suka soma gilma mata tamkar a majigi. ***** TUSHEN LABARIN! Bayan haihuwarta ta biyu ne jini ya tsinke mata, washegarin haihuwar yar ta koma ga mahaliccinta. Ita kuma ta samu matsalar da dole aka cire mata mahaifa bakidaya. Shi kadai gare ta, shi kadai Allah ya bar mata, UWAIS kenan. Mahaifinsa Justice Abdulkarim Shagari tsohon alkali ne dan asalin jihar Sokoto, wanda ya taka har matsayin Grand Khadi a lokacin rayuwarsa. Dan asalin Sokoto ne amma a Kano ya rayu sanadin aikin sa da ya samu a Kano, ya yi kuma aure da Safeeyah tun yana dalibin digiri na biyu a kasar ta Sudan inda ya yi dukkan karatunsa. Sun zauna a can shekaru biyar, sannan ya taho da ita kasarsa ta haihuwa, Nigeria, ya samu aiki da (Shariah Court of Appeal), ya sanya ta a jamiar Bayero, inda ta yi nata karatun a fannin tsimi da tanadi. Allah ya azurta su da Da guda daya, ko ace daya tamkar da goma, shi ne Uwais, wajen haihuwarta ta biyu ne waccan matsalar ta faru. Uwais na girma, sha'awarta da shaukinta ga son haihuwar diya mace na karuwa, bayan already an cire mata mahaifa. Duk inda ta ga baby mace kamar ta zauce, ita ba yan uwa a Nigeria ba balle ta karbo yar riko, cikin yan uwanta kuma da ke Sudan ta tabbata babu mai ba ta, alhalin tana kasar Nigeria. Don auren dan Nigeria da ta yi ma ba da son ransu ta yi shi ba. Larabawa akwai kabilanci. Maigidanta kullum cikin kwantar mata da hankali ya ke, don ta kara kwantar da hankalinta a kan haihuwar diya mace ya samo mata aikin koyarwa a Bayero University, ta zama cikakkiyar assistant lakcara. Ba ta dade da fara aikin ba Allah ya yi wa Grand Khadi Abdulkarim Shagari rasuwa. Mutuwar da ta gigita Safiyyah da tilon danta Uwais. An dauki lokaci kafin su dawo hayyacinsu. Kadaici ya kara yi wa Safiyya wadda danta Uwais ke kira Ammi yawa, daga ita sai danta ta ke rayuwa sai mai aikinta Talatu, wadda ta ke tare da ita tun Uwais na karami. Shaawarta ga son diya mace bai canza ba bayan rasuwar mijinta, sai ma karuwa da ya yi a dalilin rashin miji mai tattali, soyayya, kulawa da nuna kauna wato Grand Khadi Shagari. A wani dare da kadaici ya yi mata yawa, kuma ta yanke shawarar ci gaba da rayuwa a Nigeria madadin ta koma Sudan saboda aikinta, wani tunani ya fado mata..... Ita dai ba za ta iya kara yin aure ba, don Uwais baya so, ya fada ya kara, muddin ta kara aure tayiwa Babansa kishiya a bayan ran sa shi Sudan zai koma wajen Kawunsa Shuraim wato Yayanta, wanda ke da da sa'ansa mai suna Mahdi, kuma ko ta yi aure ta san ba haihuwa za ta kara yi ba, don haka ta yanke shawarar dauko ya daga GIDAN MARAYU (Orphanage). Ta hada da Uwais ta rike sun isheta rayuwar duniya, tayi musu raino da tarbiyyah irin wanda take so sannan a karshe ta yi wa kowannen su aure da wuri, su haifa mata jikokin da zasu gina mata extended family mai albarka a kasar mijin ta, Nigeria. ****** "Tsintarta aka yi, a kofar makarantar firamare ta gidan Galadima, tana jaririya sabuwar haihuwa ko wanka ba a yi mata ba, a cikin kwalin taliyar indomie, ko suttura babu a jikinta, babu wata shaida da muka samu a kanta bayan wannan". Shugabar gidan marayu na Kano wanda ke unguwar Nasarawa ta gaya wa Haj. Safiyya. Ta kara rike yar bakar yarinyar mai kyawun fuska sosai a jikinta, wadda ba ta fi shekaru uku ba. Ta cike duk wasu formalities na daukar Da a gidan marayu ta karbe ta cike da so da kauna. Tunda suka taho a cikin motar ta babban dan yatsan yarinyar nan yana cikin bakinta tana tsotso, alamu ne na cewa, yarinya ce mai tsananin hakuri. A nan kantinan da ke kallon asibitin Nassarawa ta tsaya ta saya mata sutturun yara masu yawa, sannan suka karaso gida. Ammi! Uwais da ke wajen kwallon kwando a kofar gida tare da abokansa ya fada cikin mamaki a lokacin da ya ga ta fito daga mota dauke da yarinya. Wace ce wannan? Ina kika samo ta Ya sake tambaya. Murmushi ta yi masa tare da kamo hannunsa, amma sai ya janye daga gare ta cikin tsoro. Ammi ina ki ka samo ya? Ta mika hannu za ta sake kamo hannunsa, ya kara ja da baya. Haba Uwais! Kanwa ce na samo maka, were living a lonely life, ka ga ka samu abokiyar hira da wasa idan bana nan. Kai ya shiga girgizawa da sauri da karfi. Bana so Ammi, bana son ki da wani Da ba ni ba!. Haushi ya sa ta shige cikin gida ta barshi a wajen. Talatu ta fito daga kitchen tana wa Ammi barka da zuwa, tare da karbar yarinyar da ke hannunta. Ina muka samo ya? Tubarkallah haka? Ammi ta ajiye handbag dinta a kan kujera, Kanwa ce na samo wa dan gidanki Talatu, ita ma ya ta ce daga yau. Bayan wannan har inda yau ke motsi, Talatu ba ta san ina Hajiya Safiyyah ta samo yar ta Fahimah ba. Ta san dai ba sato ta ta yi ba, amma tunda ba ta taba bude baki ta gaya mata ba sai ba ta takura mata da tambaya ba. Farat daya yarinyar ta shiga ranta, in Ammi na wajen aiki to Fahimah tana hannunta. Suka zage wajen kula da ita su biyu. Suna karba-karba in Ammi ta tafi aiki. Albashin Ammi da shi suke rayuwa cikin rufin asiri, rayuwarsu very simple, ta wadanda ilmi ya wadata. A wancan lokacin cikin gidajen malamai na sabuwar jami'ar Bayero suke zaune gidan dajami'ar Bayero ta baiwa Ammi. Sabida ya fi wa Ammi saukin zirga-zirga. Acan ta sanya Fahimah a (staff school). Lokacin Uwais ya gama ya shiga sakandire a Musa Iliyasu wadda itama nan kusa dasu take. Grand Khadi Shagari ya bar musu gadon tankareren gidan da suke ciki a halin yanzu wanda suka dawo cikin sa bayan Fahimah ta fara karatun sakandire a 'Yan Dutse College, ya bar musu gidan wanda ke unguwar 'Yankaba da tsabar kudi a banki, wanda Ammi ta sayi hanun jari da su a bankuna duk wata suna karbar kamasho. A haka ta dauki nauyin karatun yayanta guda biyu, Uwais da Fahimah! Cin zalin na duniya da mugunta iri-iri babu irin wanda Uwais bai yi wa Fahimah ba, wadda har gobe bai san a ina Ammi ta samo ta ba. Sai da ya shekara ashirin ne ya gane Ammi a gidan marayu ta dauko Fahimah, don lokaci zuwa lokaci yana kai su gidan marayu ta gaida wata mata wadda ya fahimci shugabar gidan ce. Ita kanta Fahimah ba ta san hadinta da Hajiya Asabe ba, da Ammi ke yawan kai ta ta gaishe ta in ta samu lokaci, kuma hankalinta da dan guntun tunanin ta na lokacin bai taba ba ta cewa gidan marayu gidansu ne ba. Ta fi daukar Hajiya Asabe a matsayin kawar Ammi, don in suka hadu suka tsinke da hira har ba sa son rabuwa. Daga baya Hajiya Asabe har gidansu tana zuwa, Ammi na yi mata alheri sosai. Musanman lokacin da ta zo aurar da diyarta ta fari Ammi ce ta dauki nauyin gado da kujeru. Tun daga lokacin da Uwais ya gane daga inda Ammi ta dauko Fahimah tsanarshi da ita ya karu, ya nunku. Ya tsani ya bude ido ya ganta gabansa, sabida yawan tsawar da yake mata ko hanyar dakinsa ba ta bi. Haka in yana falo ta leko ta ganshi komawa dakinta ta ke ta rufe kofa har sai ya fita. A haka suka taso, Fahimah na mamakin abin da ya sa ita nata Yayan ya tsane ta, bayan ba haka ta ga sauran yayyen kawayenta na makaranta suna treating dinsu ba. Duk ranar da uzuri ya sa Ammi ba ta dauko ta a makaranta ba, ta tura shi ya dauko ta sai ta dawo da kumburarriyar fuska, ya mammake ta a motar ko ya rarrankwashe ta. Dalili hakan ya sa Ammi daukar mata direba nata ita kadai lokacin da ta shiga sakandire a Yan Dutse. Ammi ta yi nasihar, ta yi lallashin a kan Uwais ya karbi Fahimah a matsayin yar uwarsa da Allah ya ba shi, har ta koma ta zuba ido, domin kuwa Uwais kaifi daya ne. Kuma mai gabadaya. Abin nufi; In zai so abu dukkan soyayya yake masa, haka in zai ki shi, muguwar kiyayyah yake masa bata wasa ba. Ya sha gaya wa Ammi shi ba zai taba son wannan tsintacciyar magen da ta kawo musu ba. Tun yana yaro Allah ya zuba masa baiwar kyau na larabawan ifriqiyyah, wani irin kyau mai sanyaya idanun duk mai kallon sa, ya hore masa kwakwalwar karatu musamman darasin lissafi, don haka ne da ya zo shiga jamia ya zabi ya karanta aikin banki. Ya yi digirinsa na farko da na biyu a jamiar Ahmadu Bello, inda ya karanci fannin accountancy. Bai dade da kammala karatu ba ya samu aiki da babban bankin Guaranteed Trust (GT Bank) matsayin akawu (Accountant) sabida kyawun takardunsa. Haka rayuwa ta mika wa wannan family cike da ci gaba da nasarori. Zuwa wannan lokacin Ammi Safiyyah na amsa rank na (Associate Professor) a tsangayar Economics da ta ke koyarwa. Fahimah na ajin karshe a sakandire. Uwais kullum cikin promotion yake daga bankin GT sabida kwazonsa da persevearance. A halin yanzu shine babban manajan Branch din GT da yake kan titin (Bank Road) da ke cikin birnin Kano. Ya karbi ragamar kula da komai na nauyin gidansu ban da shaanin FAHIMAH. A wurin sa kam Ammi ce kawai dangin ta. Bai taba cewa wani yana da kanwa ba. Koda dangin su na Sudan. Baya bari ma wadanda suka san shi su san da wanzuwar ta tare da mahaifiyar sa. Ya tsaya kamar shine Grand Khadi Shagari, baka taba gane babu mai gida a gidan sabida tsayuwar dakan Uwais akan komai na gidan. ***** Hajiya Safiyyah ta nisa a hankali lokacin da tunaninta ya zo nan. Ba ta haifi Faheemah ba, amma yadda ta ke jinta a zuciyarta ba maraba da yadda ta ke jin tilon danta Uwais. Abubuwa da yawa suka yi sanadiyyar wannan kauna; halayen Faheemah da matsananciyar biyayyar da ta ke yi mata. Kafin a samu yarinya nitsattsiya cikin yammata dubu irin Fahimah sai an tona. Sai dai daga ita har Fahimar sun kwana da sanin cewa babu wanda Uwais ya tsana a duniya irinta. A shekarun ta na kuruciya Fahimah ta san Hajiya Safiyyah ba ta haife ta ba, amma in za'a kashe ta, ba ta san ta ya ya aka yi ta zo hannunta ba. Ta budi ido ne kawai ta ganta a gabanta cikin wata irin kulawa wadda mahaifiya ce kadai za ta yi wa dan da ta haifa. Safiya ce mai tsananin hazo wadda matsanancin sanyin watan Nuwamba ya haifar, ranar ta kasance Litinin, aka ce ko Bature yana tsoron ki, tafe yake cikin motarsa Kia Picanto fara sol sanye cikin bakaken suit na maaikatan bankin GT, a nutse yake tukinsa kamar yadda ya saba misalin karfe bakwai na safe. Daidai lokacin da danja ta tsaida su a shateletalen Beirut Road ya rage gudun motar ya tsaya a gefen wata mota Toyota Camry. Hankalinsa na kan danja cike da kaguwar ta ba su hannu domin hakika ya kusa makara, sai ji ya yi daga gefensa an kira sunansa cikin tu'ajjibi.. 9/23/21, 8:15 PM - Buhainat: UWAIS SHAGARI?! Ya juya a hankali cikin aji irin nasa ya dubi mai kiran nasa, JABEER DIKKO. Ya kira sunan mutumin da yanayi na mamaki. Daidai lokacin da danja ta ba su hannu duk suka gangara gefen titi don su samu damar gaisawa da juna. A tare suka fito daga motocinsu suka cafke hannun juna, they have been good friends during their university years a jamiar Ahmadu Bello, bayan sun kammala ne Jabir ya samu tafiya kasar Kuwait yin masters dinshi, yayin da shi Uwais ya ci gaba a nan Ahmadu Bello ba su kara haduwa ba kuma sai yau. A gurguje suka yi musayen lambar waya da alkawarin Uwais zai zo gidansa in ya tashi ofis don shi Jabir ya yi aure ba dadewa, a yanzun yana aiki ne da FCMB. Kamar yadda ya yi alkawari yana tashi daga ofis ya dawo gida ya yi wanka ya sake shiryawa cikin shadda wagambari mai hasken sararin samaniya, inda duk ya gifta sanyin Maison Francis dinsa ke tashi. A falo ya tadda Ammi, Fahimah na murza mata menthol a kafafunta kamar yadda ta ke mata duk dare, kallo daya ya yi mata ya dauke kai, a ransa fadi yake, yarinya kullum kamar ana shafa mata shuni don baki. Ammi ta dube shi affectionately (cike da kauna) ko ita da ta haife shi in ya dau wankan nan kwarjini yake mata. Ta ce, Sai ina haka? Bayan ga abinci Talatu ta shirya maka? Ya ce "I'm sorry Ammi, an gayyace ni cin abincin dare, abokina Jabir na Kuwait da na ke ba ki labari yau Allah ya sake hada mu. Ammi ta ce, A dawo lafiya, a gaishe shi. Ya sa kai ya fita, Fahimah na satar kallonsa ta gefen idonta, kirjinta na wani irin duka. A karshe ita da Ammi suka ci abincin da ya bari din, suna gamawa ta kwashe komai ta kai kicin ta gyara wajen ta yi wa Ammi sallama cewa tana da karatun da za ta yi, sai ta shige dakinta ta kulle kanta. “Fahimah Shagari. Kamar yadda ake kiranta a makaranta, budurwa ce yar kimanin shekaru goma sha takwas da haihuwa. A bana ne za ta kare karatun sakandire. A jerin kyawawan mata ba za ka sanya Faheemah ba domin ba ta da artificial beauty irin na yammatan yanzu, komai nata natural daga kalar fata har gashin kai. Baka ce sidik, fatarta mai sulbi da daukar idanu. Tana da manyan ido mai haske da madaidaicin hanci, gashin kanta kakkarfa na asalin Hausawa wanda ba ta taba yi wa relaxing ba sai dai ta yi steaming dinsa. Bakinta dan madaidaici, ba ta a layin dogaye kamar yadda ba ta a layin gajeru, ga ta nan dai yar dagwas da ita, wadda tsafta da wanka suka kama jikinta. Fahimah ta dauko littafin Food and Nutrition daga jakarta ta makaranta da niyyar karantawa kamar yadda ta yi niyya, don tana da gwaji (test) a kansa a washegari talata. Shine kuma best subject din ta. Amma me? Ko da ta bude shafin farko ba ta ga komai a ciki ba. Shafin ya koma blank, sannan basudaniyar fuskarsa ta maye gurbinsa. Ta bude shafi na biyu don a zatonta a wancan shafin ne kadai Uwais ke yi mata shifcin gizo, sai dai duka sammakal. Cikin kowanne shafi da ta bude ba ta ganin komai sai Uwais Shagari, fuskarsa, tsayuwarsa, cin maganinsa da maganarsa cikin seriousness. A duniya ba ta taba ganin abin da ke wahalar da ita da dagula mata lissafi ya hana ta jin dadin rayuwarta ko ta ya ya irin tunanin miskilin Yayan nata, wanda bai san tana yi ba, bai san Allah ya yi ruwan tsirarta cikin gidan su ba. Ita din ba komai ba ce face abar wulakantawa, kuma abar kyama a gare shi, to a kan me ta ke yawan ganinsa cikin idonta? Take jin amsa-kuwwar husky voice din sa? Ta ke kuma jinsa har cikin ruhi da tsokar jikinta??? Za ta so a ce tana da wanda za ta iya yi wa wannan tambayar, tsakaninta da kawayenta na makaranta sabgar karatu ce kadai. Ammi kullum na gargadinta a kan tara kawaye da fada musu sirrinta, ta gaya mata ita kadai za ta mayar babbar aminiyarta, komai ta ke son tattaunawa na rayuwarta da ita za ta tattauna shi, amma wannan karon ba ta jin za ta iya gaya mata cewa tana da wani irin feeling a kan Yaya Uwais da ke takura ruhinta wanda ita kanta ta ke neman sani a kansa, ko me za ta ce? Da dai a ce ba Ammin ce ta haife shi ba shi ne za ta iya tattauna wannan alamarin da ita. A karshe karatun da ta yi niyyar yi bai yiwu ba, haka ta tattara littattafan ta maidasu jakarta. Ta koma ta kwanta a gadonta ta mike kafafu ta yi filo da hannayenta, ba don babu filon ba sai don ta fi jin dadin kwanciyar ta a haka. Ta bai wa tunanin Uwais dama ya zo ya sha sharafinsa...... yadda ya ke so, ya ci gaba da lugwigwita zuciyarta.... Idanunta a rufe ruf! Amma ba barci ta ke ba, ba ta hango komai sai surar Uwais dazu-dazu da zai fita, yana wadannan harare-hararen nasa, da maganar sa sauri-sauri da husky muryarsa mai huda mata ruhi da zuciya.... ****** Tun kafin ya gama parking Jabir da matarsa Murjanatu suka fito tarbarsa. Murjanatu ta sha lullubi a kan kwalliyarta kai daga ganinta ka ga irin mutunci, sannan kuma yar babban gida. Gidan Jabir Dikko madaidaicin flat ne a unguwar Eastern Bypass. Sun tsara gidansu shi da Murjanatu daidai da rayuwarsu ta yan boko. Ita ma Murjanatu maaikaciyar banki ce, sai dai ita tana Polaris, sun hadu da Jabir tun a jamia duk da yana gabanta sosai, hannun Jabir cikin na Uwais suka shiga kayataccen falon nasu. Murjanatu ba ta tsaya ba, ta yi ta shige da fice daga kicin zuwa falo don wadata su da dukkan abin da za su bukata wajen cin abincinsu. Suna tsaka da cin abincin ta fito daga uwardakin Murjanatu tana mika..., ga dukkan alamu ba ta san da mutane a falon ba, sannan daga barci ta tashi. Farar doguwar shimi ce a jikinta mai santsi (armless) kanta ko kallabi babu, ta matse gashin kanta mai tsayi da santsi a tsakiyar kanta. Kai ka ce jarumar nan ta fina-finan Hindi ce wato Sushmita Sen. Ga tsayi ga zati. Wuta ta daukewa Uwais na dan lokaci, ya nemi zuqar numfashi ya kasa, bai taba ganin kyakkyawan abu da ya keta zuciyar sa irin wannan halitta da ke tsaye gabansa ba. Sannan a lokaci guda idanuwansu suka sarke cikin na juna, chemistry din ya afku a lokaci guda. Amrah go and cover yourself. Ta ji muryar yayanta a tsakar kanta, a lokacin ne ta ankara da yanayin sutturar jikinta, da bakon fuskar da ke falon wanda ta zama lost a cikin kallonsa. Da sauri ta juya ta shige daki, Uwais ya bi ta da ragaitattun idanunsa. Tunda yake a rayuwarsa bai taba jin yana son mace da dukkan zuciyarsa da ruhi irin yau ba. Yes, ya yi dating iri-iri a makaranta amma bai taba jin abin har zuciyarsa ba. Yawanci ma matan ke fara kawo kansu. Yau kuwa ji ya ke ba shi da sauran buri a rayuwa irin na mallakar kyakkyawan abin da ya gani yanzun nan. Jabir na ta yi masa hira, sai ya lura Uwais absent - mindedly yake sauraronsa. Ya dan doki kafadarsa, Kai tunanin me ka ke haka ina ta magana ba ka jina? Suka ci gaba da cin abincin su, amma Uwais bai kara nutsuwa ba. Sannan dandanon abincin bai kara hawa kansa ba duk da kwarewar da Murjanatu ta nuna wajen sarrafa shi. Sai da Jabir ya rako shi zai tafi ne ya tambaye shi game da yarinyar da ya gani dazu, Jabir ya ce, Wai Amrah? Kanwata ce uwa daya uba daya, ta zo mana hutu ne, a Malaysia ta ke karatu. Duk miskilancin Uwais yau ya kasa sarrafa kansa. Ya ce, To Jabir, ko in shigo daga ciki ne? Dariya Jabir ya yi sosai ya ce, Ta yi kankanta da aure a gidan mu. Yanzu ne ta ke shekarar farko a karatunta na medicine, Daddy ya fi so ta kammala MBBS ma kafin ya yi mata aure. Uwais ya marairaice wa Jabir, Ni dai don Allah ka shige min gaba, ka gabatar da ni ga Daddy, sai da izininsa zan fara nemanta. Wallahi na yi alkawarin barinta ta yi karatu har sai ta ce ya ishe ta. Ka ji tausayi na Jabir na kai 30 fa, kullum da jikakkiyar kanwa ta a kofi a gefen gado nake kwana. Dariya sosai Jabir ke yi, dama gwanin dariya ne, ya ce, Ina su Salma? Firdaus? Jennifer and co? Ka fi karfin autar mu Uwais, you never take any dating serious, ina tsoron in shigar maka ka gano wata ka bar min kanwa emotionally touched. Uwais ya shafi lallausar sumar kansa, ya ce, Joke apart Jabir, ni fa na ga mata a gidanka. So ko ka ki supporting dina zan kai kaina ga Daddy, amanar kanwarka idan na ci ta Allah ya ci tawa. Ko daga cikin amon muryarsa Jabir ya san he is now talking serious, amma gani yake Uwais ya fi karfin Amrah domin shekarunsa sun kusa ninka nata. Ga shi da matukar wayewa tun suna jamia da farin jinin mata fiye da dukkan abokansu. Sai dai ta fannin tarbiyya ya yarda Uwais ya same ta cikakkiya. Maman shi is over-protective. Don haka ya yi masa alkawarin zai kai shi wajen mahaifinsu in ya zo gari kasancewar a Abuja iyayensu ke zaune. Yana da wata matar a nan Kano bayan mahaifiyarsu duk karshen wata yake zuwa Kano ya yi kwana uku kacal. Ko shi zai so Amrah ta samu gwarzon miji irin Uwais Shagari. Tun daga ranar Uwais ya maida gidan Jabir wajen cin abincin darensa, don kawai ya ga Amrah. Ya yi alkawarin ba zai tunkare ta ba sai da yardar mahaifinta kamar yadda shariah ta umarta. Ya kuma roki Jabir ko Murja kada ya bari ta ji don Amrah yake zuwa, shi kuma Jabir da gayya yake kiranta ya sa ta aiki in Uwais ya zo don ya samu ya ganta hankalinsa ya kwanta. Girkin ma cewa yake Murjanatu ta sakar mata don Uwais ya ce ba abin da yake so irin ya ci abin da ta sarrafa da hannunta. A fannin ita Amrah ba ta san manufarsu ba, don haka da zuciyarta daya ta ke yin komai da Jabir ya sa ta yi musu. Murja dai duk da Jabir bai gaya mata don Amrah abokin nasa yake zuwa ba ta fara ramfo su, ko tsakiyar idanun Uwais ka kalla sai ka ga kwantacciyar soyayyah. Cikin kallon da yake yi wa Amrah. A ranta dari bisa dari tana supporting abun don har zuciyarta ta san in Amrah ta yi nasarar samun Uwais a matsayin miji ta yi matukar dacen miji daya da daya a cikin maza. Yawan fitar da ya tsira kullum bayan ya dawo ofis wanda a baya ba ya yi kuma ba halin sa bane ya soma damun Ammi. Ta tsare shi da tambayar ina yake zuwa ko abincin dare ba ya ci a gida? Ya ce mata babu inda yake zuwa sai gidan Jabir dole ta kyale shi. Ranar jumaa Alhaji Umar Dikko ya sauka garin Kano daga birnin tarayya. Gidansa na Kano yana unguwar Bompai. Tsohon dan boko ne da aka dade ana damawa da shi a gwamnatin tarayyah, a halin yanzu shine shugaban hukumar Haraji ta kasa. Yayansa takwas biyar ciki daya, uku ciki daya, Jabir ne babba, sai Hassan da Hussaini, Wasila sannan autarsu Amrah. Amaryarsa da ke Kano tana da yaya uku kanana. Sun yi shi da Jabir cewa in daddy ya sauka jumaa, washegari asabar za su je su same shi da kokon barar su. Duk da Jabir ya san mawuyaci ne Baban nasu ya amince ya aurar da Amrah a wannan lokacin. Sai dai an ce a rashin tayi akan bar arha kuma a rashin kira karen bebe ya bata. Tun karfe bakwai yake shiri, kayan da ya tanada musamman don ranar babban riga da yar ciki da wando na wani rantsattsen yadin filtex milk colour ya sanya ya feshe su da 'Maison Francis' dinsa. Agogon rolex mai fata ruwan kasa-kasa ya daura a damtsen hannunsa, haka hular kansa da budadden takalminsa ALDO duk ruwan kasa-kasa ne. kowa ya kalle shi sai ya kara, ya hadu iyakar haduwar da kowacce rantsatstsiyar mace ke buri a mijin aurenta. Uwais Abdulkarim Shagari kenan. A falo ya tadda Ammi da Fahimah suna shan shayin da ba ya rabo da gaban Ammi. Fahima sanye cikin wani lallausan cotton lace ruwan makuba mai ratsin orange, ta kalmasa daurin kai mai tsari a kanta kamar mai shirin zuwa dinner. Nan kuwa daga ita sai Allah Ubangijinta suka san don wa ta yi kwalliyar nan, a daidai lokacin da ta tabbatar zai fito ya tafi yawon magribarsa da ya tsira kwanan nan. Bayan ya yi mugun daukar wanka. Ita a kan karan-kanta ba maabociyar kwalliya ba ce, kuma ba ta yinta sam a fuskarta, amma tana zama ta bata lokaci wajen kalmasa daurin kai mai tsari wanda zai fiddo cute fuskarta, da lace ko atamfa (her fovourite attire). Ta shafa wet-lips mai kamshi da tausasa lebe. Burin zuciyarta in zai shige ta ganshi, ko da ba zai kalle ta ba, ita za ta saci kallonsa zuciyarta ta rage zugi da radadin da ta ke mata a kansa. Sai ina kuma? Wannan babbar riga haka? Ammi ta fada trying hard ta tuna lokaci na karshe da ta ganshi cikin babbar riga. Baki sake ta ke kallonsa don alamuransa a dan tsukin nan ta kasa gane musu. Kamar wanda yayi gamo sai aukin wanka kamar kwado. Wani sassanyan murmushi ya yi, a miskile ya ce, Ammi, neman aure za ni, ki yi min addua. sai na dawo. Bai jira cewarta ba ya sa kai ya fice. Ammi ta bi shi da sakakken baki kafin ta ce da Fahima, wadda ta daskare a wurin, Anya Uwais lafiyarsa? Aure? A ina? Ba don bai kai munzalin ya yi auren ba ne ya sa Ammi ta yi wa kanta wannan tambayar ba, sai don kallon da ta ke masa na miskilancinsa ba zai taba bari ya taba cewa yana son mace ba. Sai fargawa ta yi babu Fahimah a wajen, ta shige dakinta ta bame kofa. Tana rufe kofar ta jingina jikinta ta lumshe idanunta tana amsar sababbin feelings din da maganar Uwais ta haifar. Masu kama da fitar bullet zuwa tsakiyar kirjinta. AMMI NEMAN AURE ZA NI! She dont actually know the meaning of the feelings, amma ta san it deeply hurts, some hidden parts da ke karkashin zuciyarta. Neman aure za ni, Ammi ki yi min addua. Maganar Uwais ta yi amsa-kuwwa a cikin kanta a karo na biyu, ta kuma rasa dalilin da ya sa ta haifar mata da wannan bitterness din a kasan ranta. Me hakan ke nufi? Zuciyarta na nufin Uwais ba zai yi aure ba? Ko kuwa bai kai munzalin yin aure ba? Amma da ta yi tsam da ranta da hankalinta waje guda a yau, sai ta fahimci cewa Uwais zuciyarta da gangar jikinta ke son aure, wanda hakan na nufin zuciyarta LOVES UWAIS DEARLY..... shine dalilin da yasa taji wannan bitterness din a karkashin ranta don ya ce ya tafi neman aure. Da ta ki da ta so gaskiyar magana kenan, shi ne kuma fassarar duka unexpressable feelings din da ke dankare cike da zuciyarta shekara da shekaru akan Yaya Uwais, shi ne kuma silar jin abin da ta ke ji yanzu da ya ce ya tafi neman aure, something unbelievably like KISHI. A hankali Fahima ta sauke ajiyar zuciya tana jin tamkar zuciyarta na gutsittsirewa into pieces tana narkewa kamar dalma, kawai saboda Uwais ya ce ya tafi neman aure! To ina ga ranar da aka daura auren sa da wata akan idon ta!? Da kyar ta ja kafa zuwa gadonta ta kwanta rigingine, abubuwa da yawa na gilmawa a idanunta.... zuciyarta na hasko mata ranar da za ta ga matar Uwais a gabanta, ko how does she look? Ta tabbata She must be beautiful like him in one way or the other.....ba kamar ita ba, and the LUCKIEST woman on earth...... watakila ranar ce ranar karewar numfashinta a duniyar Subhana......(ranar da zata ga matar Uwais). ****** 9/23/21, 8:15 PM - Buhainat: Kwana uku bayan nan suka wayi gari da bako na ba-zata, kawu Shuraim daga Khartoum. Ko kusa Ammi ba ta kawo a ranta abin da ya kawo Shuraim har Nigeria a kan maganar auren Uwais ne ba. Rabon shi da kasar Nigeria an fi shekaru ashirin, tun rasuwar Baban Uwais, bayan nan kuma sau daya ya taba zuwa tun Uwais na yaro don kawai ya gan shi, sai kuma yau da ta ganshi a falonta bisa jagorancin Uwais ba zato ba tsammani. Ammi ta rasa ina taka saka ina taka aje da Yayanta. Ta cika shi da cima ta alfarma. Ta sa Talatu ta gyare masa dakin baki, amma tun a wajen cin abinci ya gaya wa Ammi kwana uku kawai zai yi ya koma Sudan. Sai dare suka samu zama officially ita da Kawu Shuraim. Ta tambayi duka yan uwanta da yayansu, ya tabbatar mata kowa lafiya, sannan ya ba ta jakar himilin tsaraba da yan uwanta suka aiko ya kawo mata, wadda duk ta danganci cimar kasar Sudan da kayayyakin amfaninsu na yau da kullum. Kawu Shuraim ya yi amfani da hikima irin ta manya bai nuna Uwais kararta ya kai ba, ya ce, Safeeyyah abin da ya kawo ni takanas kasarku ba komai ba ne face maganar auren Uwais. Sai yaushe ki ka shirya yi masa aure, ko ko shi ke nan don ba mahaifinsa sai ki yi ta zama da shi a cikin gida har sai ya zama tuzuru? In matar ce bai samu ba a duba masa a can Sudan cikin yayan dangi. Da sauri Ammi ta ce, Ko kusa, ba mace ce bai samu ba, hasalima ni na dade da tanadar masa mata, ina jira ne ta kare karatun sakandire a daura musu aure. Sai kuma ya kawo min wani zancen banza wai kanwar abokinsa yake so zai aura, ni kuma na soke zancen tuntuni. Ba zan gaji da cewa mace ko da zubarjadu da yaqutu aka kerata ba za ta auri Uwais ba face Fahima ta. Kawu Shuraim ya yi murmushi, ya ce, Wace ce ita Fahimar? Ta ce, Fahima tawa dai da ka sani, wadda na dauka tun tana yarinya. Ta gidan marayu? In ji kawu Shuraim cikin shagube. Ammi ta yi shiru, ya ce, To su waye madaura aurenta, kuma su waye suka kawo ta duniya? Idan yar zina ce fa? Sai ki hada da tsarkakakken Dan ki? Wannan halaka kai don farantawa wani da me ya yi kama? To ba da mu za a yi wannan danyen kazamin aikin ba. Idan mafarki ki ke ki farka. Gobe insha Allahu zan sa shi a gaba ya kai ni har Shagari wajen dangin mahaifinsa. Mu hadu mu je mu nemo masa aure na mutunci da martaba. Tun wuri ki san yadda za ki yi da bakar yar ki, Uwais ba zai karba bayafi karfin ta Kawu Shuraim bai ankara ba sai jin shesshekar kukan Ammi ya yi a hankali ta ke kuka mai motsa zuciya. Kafin ta share hawaye ta dago ido ta dubi Yayanta. Alummar Annabi ina za ku kai rashin adalci? Su wadannan yaran me ye laifinsu? Zabin su ne zuwan su duniya a haka? Ko kuwa laifin iyayen su? Har ce mata ka ke BAKA don kawai kuna farare larabawa, shin zabinku ne fitowa da farar fata? Ko kuwa tsarinku ne irin halittar da ku ke so Ubangiji ya baku? Ni a wajena HALIN MUTUM shi ne yake sa wa a so shi, amma ba nasaba ko zubin halitta ba. Don haka in har ni na haifi Uwais na kuma raine shi ba tare da taimakon kowa ba, Fahimah na yarje masa ya aura. Duk da jikin Kawu Shuraim ya yi sanyi, amma bai ji dadin kalamanta na karshe ba, Safeeyyah ni ki ke gaya wa ke kadai ki ka raini dan ki ba tare da taimakonmu ba? Ta girgiza kai da sauri, Ka yi hakuri dan uwana, ban fada da wannan manufar ba, amma idan har kun amince, Uwais zai auri Fahimah, ni ma na yi masa adalci ya hada su ita da zabin ran nasa ya aura. Amma ita Fahima zan ci gaba da rikonta a wurina sai ranar da ya zo min da bakin sa ya ce ya karbi auren ta, burina kawai ya kasance da auren Uwais a kan ta, kuma da aurenta za ta yi karatun jamia. Duk ranar da ya ankara cewa zabi na gari na yi masa, kuma ya shirya karbar matarsa sai ya yi min magana in kai ta dakinta. Kawu ya ji dadin adalcin da Ammi ta yi wa Uwais a dalilin sa. Ya sa mata albarka, ya ce kuma insha Allahu zai yi convincing Uwais ya amince da tsarinta. Amma ko da Kawun ya yi wa Uwais bayanin da Ammi ta yi a washegari da safe, Kawu Shuraim na ganin yadda gumi/zufa ke barkowa daga kowacce kafa ta jikin Uwais kamar bai taba jin abin da ya girgiza shi irin wannan ba. Don haka Uwais ka amince kawai, ban ga laifi cikin hukuncinta ba. Mahaifiyarka ce da ta fi kowa hakki a kanka. Hakkinka ne ka faranta mata don samun aljannah. Na yarda va karamin so take yiwa yarinyar nan ba, domin kuwa har hawaye ta zubar a gabana. Ta ce ba za ka dau yarinyar zuwa gidanka ba sai sanda ka shirya karbar auren ta, zuwa lokacin Uwais kana tare da matar da ka ke so kun hayayyafa, wannan auren garkuwa ne kawai ga yarinyar kamar yadda na fahimci yar uwata. Uwais kowa ya rufa wa wani asiri, Allah zai rufa nasa. Uwais Da na kowa ne, kuma samun uwa irin taka sai an tona. A kan wannan marainiyar sai ka ga ta shiga aljanna kamar kiftawar ido mu muna gefe muna jan gindi a kan siradi, saboda girman kan mu da rashin tausayi. Haka Kawu Shuraim ya ci gaba da yi masa nasiha da nusar da shi muhimmancin biyayya ga iyaye, musamman UWA, musamman ga su maza. A fatar bakinsa bai ce ya amince zai auri Fahimah ba, amma shirun da ya yi da sunkuyar da kansa da ya yi na lokaci mai tsawo ba tare da ya ce komai ba, ya tabbatar wa Kawu Shuraim ba shi da ta cewa wai barawo a hannun mata. Don haka Kawu ya yi ta sa masa albarka ya ce ya yi musu shirin tafiya Shagari washegari, ba zai bar kasar ba sai an karba masa auren Amrah tare da shi, sannan shi zai zama waliyyin Fahimah idan lokaci ya yi ba don komai ba sai don shima yana kwadayin irin ladan da yar uwarsa ke kwadayi. Washegari ta jirgi suka tafi Sokoto shi da Kawu Shuraim, inda suka hadu da Baffaninsa na can Malam Haruna da Malam Sufyan wadanda kanne suke ga marigayi mahaifinsa Grand Khadi Shagari suka wuce Abuja gidan su Amrah. Alhaji Omar Dikko ya yi musu tarba ta mutunci, aka tattauna a kan siyasa kafin su gangaro ga abin da ya kawo su, wato nema wa dan su Uwais auren diyarsa Amrah, Kawu Shuraimn bai fadi zancen Fahimah ba kada su rusa neman auren ta hanyar bata rawar su da tsalle. Alhaji Omar Dikko ya ce, A da ban yi niyyar aurar da Amrah nan kusa ba, amma sabida yadda na ga Uwais da gaske yake sonta, sannan ya amince ta ci gaba da karatunta a Malaysia in ta yi hutu sannan ta zo masa, ko shi ya je, to ni ma na amince. Amma in za a saba wannan yarjejeniyar tun wuri a yi hakuri kawai sai ta kammala". Kawu Shuraim ya ce, an riga da an wuce wurin, domin Uwais ya amince, kuma su da komai nasu suke tafe, lokaci kawai suke so a sanya musu. A takaice ba su bar Abuja ba sai da aka tsayar da ranar daurin aure watanni uku masu zuwa, lokacin ita Amrah ta samu hutu tana gida. Hatta sadaki da kudin aure sun biya. Farin cikin da Uwais ya samu kansa a ciki ya mantar da shi zancen wata Fahimah. Bai kara tunawa da zancenta ba musamman da ya daina ganinta ma kwata-kwata. Ta daina zaman falo don karatu ya yi mata zafi. Nan da sati biyu za su fara WAEC kullum tana dakinta tana bitar littattafanta. Zuwa yanzu Fahimah ta san zuciyarta ta samu sukuni daga duk wani kalubale dake addabar ta a baya, sabida karatu ya dauke mata hankali, amma na awa daya ba ta taba manta Uwais ba. Kullum yana nan like a zuciyarta sai dai tunanin nasa ba ya hana ta sukuni kamar da, kuma ba ya hana ta fahimtar karatu, sannan ba ta da masaniya a kan batun aurensu, wanda ko a mafarkinta ba ta kawowa. A haka ta fara zana WAEC cikin dimbin nasara, ta gama ta yi NECO sannan suka zauna suna hutawa kafin su zana jamb. A can gidan Alhaji Umar Dikko gagarumin shiri suke na bikin Amrah, don ana ji da Amrah a familyn. Tuni Aunty Murjanatu da Yayarta Aunty Wasila suka karbi kudi wajen Daddyn suka tafi Dubai don hado mata kayan daki. Shi ma Uwais a nasa bangaren yana ta nasa shirin, ya kammala ginin gidansa da ke unguwar Sultan Road a Kano, gida madaidaici daidai babban maaikacin banki. Amma fa komai na mace daya ne a gidan, kuma na mace daya ake ci gaba da yi. Ba ya son tuna zancen wata Fahimah domin amai ne yake taso masa a duk lokacin da ya tuna wai tare zai aure su ita da Amrah.... Ban da uwa-uwa ce wa ya isa ya yi masa wannan kutsen cikin rayuwarsa? A nasu bangaren, Ammi da yarta Fahimah babu wani shiri da suke yi, sun ci gaba da rayuwarsu as normal as before. Ita Fahimah da ma ba ta san me ake yi ba, ko da wasa Ammi ba ta gaya mata ba. Ta san in ta yi mata umarni ba za ta tsallake ba, amma ta zabi kawai ta yi shiru akwai lokaci mafi dacewa da ya kamata ta fada matan ba yanzu da ta ke fama da jarrabawa ba. Haka ta je centre din da aka tura ta ta zana jamb dinta lami lafiya. Fahimah ta yi sallama da Yan Dutse da kawayenta da suka yi zaman aminci musamman Majida Salisu. Ya zama kullum tana gida, amma sam ba sa haduwa da Uwais. Yanzu ta daina lekensa in ta san zai shigo gaida Ammi, daga ta ga karfe shidda na yamma ta yi, ta yi sallama da falo kenan. Don ta san duk inda bakwai na magriba ta yi yana cikin gidan. Da ma sun fi haduwa da safe, in ta fito za ta tafi makaranta, shi ma ya fito zai tafi aiki, to ita yanzu ta yi sallama da makaranta. A hankali ta ji zuciyarta na samun sauki daga azalzalarta da ta ke yi a kan Uwais infatuation din yana raguwa musamman da ta daina ganinsa. Yau saura sati biyu kenan daurin aure. Ammi ta gaya masa yadda ya yi wa Amrah kayan aure, haka zai yi wa Fahimah, adadin sadakin da ya biya na Amrah haka zai biya na Fahimah. Bai tanka ta ba a lokacin da ta ke maganar, amma zuciyarsa ta yi bakikkirin, sai babbakewa ta ke kamar ta kama da wuta. Musamman ya kira Jabeer ya ce, yana son ganin Murjanatu, Jabeer ya yi masa iznin zuwa, suka zauna yana tambayarta dukkan favourite abubuwa na Amrah, colour da design da size. Ita Murjanatu ya bai wa kwangilar hada komai don ta fi kowa kusanci da Amrah. Amma ya roke ta kome ta saya ta sayi guda biyu kala ba daya ba kuma girma daya. Murjanatu ta so ta yi mishi tambaya kan hakan ta fasa. Don a yadda suka tabbatar Uwais na son Amrah, tunanin aurenta tare da wata ko yi mata kishiya ba zai taba zuwa kansu ba. Cikin sati daya Murjanatu da kawarta suka hada komai na gani na fada irin nasu na 'yan gayu ya zo a kwashe saitin akwatunan a booth din motarsa ya kai wa Ammi, sai da ya yi sawu biyu sabida dozen biyu ne akwatunan, kowacce sha biyu, samfurin LV (Louis Vuitton). Ammi ta yaba da kayan ta ce masa kowace ce ta hada kayan ta san abu mai kyau da quality, ya ce, "Murjanatu ce matar Jabir". "To Allah ya shi albarka". In ji Ammi. Talatu Ammi ta sa ta kwashe kayan ta kai dakin Fahimah, ta ce ajiya ce ta ajiye mata. Talatu ta san komai, kusan ta fi kowa farin ciki da wannan hukunci na Ammi, don kullum tana zama ta yi tunani mai zurfi a kan auren Fahimah zai zamo kalubale mai girma ga rayuwarta. Don haka hukuncin Ammi shi ne daidai ko da mata goma Uwais zai aura in dai zai hada da Fahimah hankalinsu ya kwanta. Talatu ta zarce matsayin 'yar aiki a gare su don ko kudin aiki ba ta karba, shekara da shekaru sai ihsanin da Ammi ta ga damar yi mata. Ta zame musu kamar 'yar uwa ta jini. ****** Aka ce rana ba ta karya sai dai uwar diya ta ji kunya. Kwanakin daurin aure na matsowa, soyayya gangariya na karuwa tsakanin Uwais da amaryarsa Amrah talkless of Fahima da ba ta cikin lissafin sa. Ya kama gobe daurin aure, wanda za a yi a gidan Alh. Umar Dikko na Kano, tun jiya kawu Shureim da manyan 'ya'yan sa biyu Mahdi da Mohamed da kannen Ammi biyu su biyar kenan suka iso daga Khartoum, sai mutanen Shagari kwansu da kwarkwatarsu. Duk Uwais ya yi musu masauki a gidan saukar baki na Tahir Guest Palace. Yana zaune a kujera gefen Ammi, sanye cikin wani lallausar voyel milk colour kansa babu hula, sumar nan ta kara kwanciya sosai, ta kuma kara cika da yawa domin ya dade bai rage ta ba. Ammi na daga gefensa tana shan shayin da Fahimah ta dafa mata ta kule a daki musamman da ta san Uwais zama zai yi a falon. Wayoyin jama'a yake ta amsawa kala-kala, duk a kan shirin daurin auren gobe. Sai da Ammi ta fahimci ya tsagaita da amsa wayoyin ta kira sunansa. "Uwais!". Ya dago lumsassun idanunsa ya dube ta. "Gobe nan ne wurin haduwa (meeting point) na daurin aure kafin ku tafi gidan su yarinyar?" Ya amsa mata da "Eh, Ammi". Ammi ta ce, "tam... To aurenka da Fahimah za a fara daurawa, ina nufin Fahimah ita ce za ta zama uwargida, sannan a yi na ita MATAR SO". A yadda ta fadi maganar cikin shagube ya yi bala'in touching dinsa. Sai dai ya yarda da abin da ta ce din, "Eh, Amrah matar so ce, ta ki 'yar kuwa matar shige wadda anka ce ba ta daraja sam". Bai ba ta amsa ba sai ma tashi da ya yi ya bar wurin. Ta san za a rina, da ma ba ta tsammaci ya tankata ba, umarni ta bayar kuma dole a bi in ana son zaman lafiya. Ta kira Kawu Shuraim da madaurin aurensa su Baffa Haruna duk ta gaya musu hakan, su Baffa Haruna sun yi mamaki matuka, amma da Kawu Shuraim ya yi musu bayanin komai sai suka fahimta. Washegari kofar gidan Late Grand Khadi Abdulkarim Shagari ya dinke da jama'a ko ta ina, musamman ma'aikata GT na Kano. Aka daura auren Fahimah Abdulkarim Shagari da Uwais Abdulkarim Shagari a kan sadaki mafi kankanta amma mafi albarka. Daga nan suka zarce gidan Alh. Umar Dikko aka daura na Amrah Umar Dikko da Uwais Abdulkarim Shagari. Daga nan shi da ma'aikatansa da abokansa suka wuce liyafar cin abinci ta bayan daurin aure wadda abokai suka shirya karkashin jagorancin Jabeer, a gidan saukar baki na Ni'ima. Uwais farin cikin da yake ciki a yau ba zai misaltu ba, biro ya yi kadan ya bayyana shi. At last ya mallaki AMRAH so duk wani kalubale, duk wani bacin rai zai zamanto nafilah. Suna fitowa daga wajen liyafar ya kebe kansa a gefe, Amrah ya kira. 9/23/21, 8:15 PM - Buhainat: Cikin wani yanayi ta ganta tare da Yaya Uwais, yanayin da ya fi kama da muamalar auratayya.... it is something which goes far beyond mere explanation..da fatar baki but extent reality cikin idanunta, kamar ido biyu ba mafarki ba; mafarki ta yi ma ga ta a matsayin matar Uwais, sabida abinda ta gani yana faruwa cikin mafarkin ta sani baya yiwuwa sai da aure. A karshen mafarkinta kuma ta ga yaya rututu zagaye da su, wadanda har ba ta iya kirga su ba sabida yawansu ya cika dakin da suke ciki. A matukar firgice fahimah ta farka, jikinta ba inda ba ya rawa, a karshe ta mike zuwa toilet ta sakarwa kanta shower ta ruwa mai dumi ko ta samu karkarwar da jikinta ke yi ya tsaya, ko ta samu ta yi regaining consciousness dinta. Barcin da ba ta koma ba kenan har rana ta fito. Tana kwance lamo a cikin bargo, ta kasa fita taya Talatu aiki yadda ta saba, kasancewar yau lahadi ba ta da makaranta, kuma ta yi sallar asuba da azkar dinta na safiya, sai kawai ta ci gaba da kwanciyarta. Karfe goma na safe Uwais ya fito daga bangarensa zuwa sassan Ammi, ya same ta tana sallar walha, sai ya samu gefen gadonta ya zauna yana tsumayinta har ta idar, ta yi addua suka shafa tare. A yadda Hajiya Safiyya ta ga fuskar Uwais yau, tana wani irin annuri ta tabbata yana dauke da labarin da ya faranta ransa. Ya sauko daga gefen gadon ya dawo daidai kafafun Ammi ya zauna. Ko daga irin zaman da ya yi Ammi ta fahimci muhimmiyar magana ta kawo shi. Ya ya aka yi ne ka zo ka sa ni a gaba yau Lahadi ma me ya fiddo ka da wuri haka? Na dauka duk lahadin karshen mako sai sha biyun rana ka ke fitowa? Uwais ya gyara zamansa sosai ya ce, Ammi na kasa barcin ne, sabida ina cikin farin ciki, Amrah ta amince min in tura magabatana a yi maganar aurenmu. Ba sai ta kare karatu ba. Ammi ta dube shi da sakakken baki, idonta na wani irin budewa ta ce, Wace ce haka? Kansa a kasa ya ce, Yarinyar da na ke nema, kanwar Jabir, na dade da gaya miki ina neman aure. Hajiya Safiyyah ta yi masa wani irin sakaran kallo, ta ce, Uwais! Da kakkausar murya. Da sauri ya dago ya dube ta cikin tsananin fargaba. Ta ce, Ba kanwar abokinka ba, ko kanwar shugaban kasa ce ban yarje maka aurenta ba. Mace ko da zubarjadu da yakutu aka kera ta haka za ta ganka ta barka, don tuntuni kana da matarka. Kalaman karshe tamkar saukar alburushi ya ji su a kirjinsa. Hajiya Safiyyah ta ci gaba da cewa, Da ma na zuba maka ido ne in ga iya gudun ruwanka, wannan rawar kan da ka ke a kan yarinyar nan kadai zai hana ni yarda da batunta, don na san muddin ka aure ta ba za ka taba yi wa FAHIMAH adalci ba! A matukar razane kuma a firgice Uwais ya dago ya dubi mahaifiyarsa. Fahima? Fahimah! Fahima!! A ina ya taba jin wannan sunan??? Kamar kullum yana jinsa cikin gidan nan. Daga bakin Talatu da Ammi. Cikin wani irin rashin kuzari yake kallon mahaifiyarsa. Ammi, I didnt get you right, wallahi ban gane maganar da ki ke yi ba. Hajiya Safiyyah ta mike tsaye tana nade sallayarta, In ma ka gane ai cewa za ka yi ba ka gane ba, sabida rainin hankali irin naka Uwais, tunda dai ni da Hausa na yi maganata. In hausar ce ba ka ji sai ka je ka nemi wanda zai fassara maka. Ta fice daga dakin ta barshi nan a zaune. Uwais ya ci gaba da zama a inda ya ke tamkar an kafe shi. Kokari yake ya yi digesting maganganun Ammi cikin kwakwalwarsa abu ya gagara. Allah ne ya kawo Talatu wadda yake kira "Baba Talatu" da tsintsiyar kwakwa a hannunta za ta yi wa Ammi shara. Ta ganshi a zaune kamar statue, ta ce, Uban masu gida tunanin me ake haka? Can tsakiyar kansa ya jiyo muryar Baba Talatu, ji ya yi tamkar mai fassarar da Ammi ta ambata ce Allah ya kawo masa. Talatu couldnt believe cewa muryar Uwais ce ke yi mata magana, sabida yadda ta sirance ta zaftare, duk wani thickeness da huskness da ke cikinta ya tafi. Baba Talatu idan aka ce mutum tuntuni yana da mata me ake nufi? Tambayar ta bai wa Talatu dariya, ta ce, Ubangidana ana nufin yana da matar aure ko? Abin da ban fahimta ba shi ne, an yi auren ko za a yi ne nan gaba? Uwais ya hadiyi miyau kamar ya hadiyi kunama, ya ce, Baba Talatu wace ce FAHIMAH? Talatu ta kai idonta da sauri ga hoton Fahimah da ke gefen gadon Ammi daidai inda ta ke saka kanta. Ta ce, Uban masu gida, Fahimah ai daya muke da ita, kuma daya muka sani wata ce ban da abokiyar haihuwarka? Ina nufin Fahimah ta gidan nan, autar Ammi. A lokacin ne kwakwalwar Uwais ta soma daukan caji, ya ji wani irin bacin rai da bakin ciki sun zo sun tokare shi a kahon zuci. Bai yi aune ba ya ji cikinsa na hautsinawa Talatu ba ta ankara ba sai ganin Uwais ta yi yana kelayo amai a tsakar dakin Ammi. Amai sosai ya yi kamar zai amayar da yan hajinsa. Talatu sai faman sannu ta ke masa ya tashi yana rangaji ya bar dakin ba tare da ya karbi ruwan da ta kawo masa daga firji tana fadin ya wanke fuskarsa ya kurkure baki ba, zai ji dan dama-dama. Ta gaban Ammi ya wuce fuuu tana zaune a falo, ko kallon fuskarta bai yi ba ya wuce, abinda bai taba yi ba. Ammi ta kyabe baki ta dauke kanta daga bayan sa. Ba don aikinsa ba yau zai bar garin. Tafiyar da sai Ammi ta janye mummunan furucinta sannan ya dawo. To Banki ba su san excuse ba. Yau yayi nadamar zabar aikin banki matsayin career din sa. Amma ya kudire a ransa cewa Ammi ta samu matsala irin ta cutar dimentia wadda tsofaffi ke fama da ita. Zai yi kokari ya nema mata magani. Tun daga ranar gidan ya koma wani iri ba dadi, kowa ba ya cikin walwala. Ammi ranta a mugun bace yake da maganar auren da Uwais ya rakito, Fahimah ciwon so ya gama kassara ta, ya karar da kuzarinta, ya tafi da duk wani karsashi da ta ke da shi a cikin gidan ko falo ta daina fitowa. Yayin da Uwais yana can yana neman mafita, ga balain da ke shirin tunkaro shi yo bala'i mana! Rashin Amrah ai catastroph ne, haka zancen da Ammi ta yi (abin amai), shi ma babban balaI ne a gare shi. Don in ya tabbata Ammi ba ta da dimentia kuma tana nufin abin da ta ke fadi ne har zuciyarta wace irin mafita zai nema wa kansa ba tare da ya fada fushin Ubangiji ba? Ammi ba uwa ba ce kadai, Uba ce, dangi ce, abokiya ce komai ce a gare shi, amma ba zai iya yi mata wannan uzurin ba, ko da duk duniya za ta taru a kanshi. Zai iya hakura da Amrah in abinda auren ta zai janyo masa kenan, amma auren Fahimah sai dai ayi da gawar sa. ****** Walwalar gidan duk sai ta ragu, kowa yana dakinsa kullum, Talatu ce kadai ke shige da fice don tsaftace muhalli, abinci sun daina ci tare a dining yadda suka saba, sai dai ta kai wa kowa dakinsa, ta kuma lura ko ta kai din ba wani cin kirki suke masa ba kamar da, musamman Uwais ko tabawa ba ya yi, in ya fice tun bakwai na safe sai bakwai na magriba ko a ofis coffee kawai yake sha wanda yake hadawa da kansa. Amrah ta koma Malaysia tuntuni, kullum suka yi waya tana jin muryar Uwais ba yadda ta saba jinta ba, ko da ta tambayi dalili sai ya ce mata, Aiki ne yake masa yawa. Yanzu ya rage zuwa gidan Jabir tun bayan komawar Amrah, tsiya iri-iri Jabir ya masa amma sai dai kawai ya yi murmushi ya ce, To me zan zo in yi maka, kai ma ka san ba don kai nake zuwa ba. Ko kusa bai gaya masa yana da matsala da Amminsa a kan maganar Amrah ba. Yau yana ofis kawai wani tunani ya fado masa, Kawu Shuraim. A kasar Sudan, shi ya fado masa a rai, Yayan Ammi da suke uwa daya uba daya, kuma wanda Ammi ba ta iya tsallake maganarsa. Wata ajiyar zuciya Uwais ya saki, ya mika hannu ya dauko wayarsa a kan tebir din gabansa ya lalubo lambar Kawun nasa. Uwais na nan da larabci zam a bakinsa, don Ammi tana yi masa sosai tun yana yaro. Sannan akwai aminci sosai tsakaninsa da Kawun nasa don yana yawan yi masa alkhairi ba tare da sanin Ammi bama. Shi kadai ya rage babba a family din su Ammi, ya manyanta, ragowar duk kannenta ne maza da mata. Suka gaisa sosai da Kawun, shi da kansa ya tsinkayi damuwa a muryar Uwais, ya ce, Uwais gaya min ko me ke damunka, insha Allahu za'a samu mafita. Uwais ya runtse idonsa ya ce, Kawu, matar aure na samu wadda nake so, daidai da ra'ayi na, mai duk qualities din da nake bukata a matar aurena, ina sonta sosai, kuma ta amince min in turo magabatana yanzu haka. Da na zo na gaya wa Ammi, sai ta kawo wani batu wanda har yau na kasa daidaita maanarsa a kwakwalwata. Kawu, na dai fahimci wai ta yi min mata ne already, imagine Kawu da wannan tsintacciyar magen da ta dauko a gidan marayu. Yaa Subhanallah! In ji kawu Shuraim cikin kakabi. Ya ce, Ita Safiyyar da hankalinta za ta aura maka wannan bakar yar mara asali? Kamar matan Sudan da na Najeriya sun kare? Uwais ji ya yi kamar Kawunsa ya yayyafa masa ruwa a kan wutar da ke tiriri a kirjinsa, ya ce, Kawu na saya maka tiket, don Allah ka zo a yi ta ta kare. Kai kadai ne last hope dina Kawu, don Allah ka taimaka min ka gaya wa Ammi ta aura min mata hudu a rana daya in dai da Amrah a ciki, amma ta cire wannan yarinyar a cikin su zan iya hadiyar zuciya na mutu. Da sauri Kawu Shuraim ya ce, Zan zo cikin satin nan insha Allahu, abin bai kai haka ba, ka kwantar da hankalinka. Ammi ba ta san me suke kullawa shi da Kawunsa ba. Yanzu ta fara maida walwalarta tana harkokinta cikin gida, amma ta cire Uwais daga shirginta, musamman da ta lura shi ma ya dauki gaba da ita. Damuwarta yanzu a kan Fahima ne, wadda ke ta faman ramewa babu gaira babu dalili, kuma ba ta son cin abinci. Ga jarrabawarsu ta barin sakandire na tunkaro su. Wajen karfe goma na dare, Ammi har ta yi barci ta farka, so ta ke ta binciki halin da Fahima ke ciki a daren nan. Ta sauko daga gadon ta a hankali ta daura laffayarta kamar wadda za ta unguwa, sannan ta nufi dakin Fahimah. Tun daga bakin kofa ta ke jiyo shesshekar kukan Fahimah ta karasa da sauri ta murda kofar ta shiga. Ta kifa kai a kan filo ta dunkule jikinta sai kuka ta ke. Sai jin muryar Ammi ta yi a kanta. Fahimah! Yau sai kin gaya min abin da yake damunki. Wani ke yi miki abin da ba ki so cikin gidan nan ko kuwa kin gaji da zama da ni ne? Fahimah ta dago a hankali cikin tsananin faduwar gaba, ba ta taba tsammanin Ammi a wannan lokacin ba, she will never shed tears a gaban Ammi, don haka tashin hankalinta a yanzu shi ne ganin kukanta da Ammi ta yi fiye da damuwar da ta ke ciki. Hajiya Safeeyyah ta zauna a gefen gadon ta ce, Fahima ta ba ki da wanda ya fi ni duk fadin duniyar nan, don haka daure ki gaya min ko mene ne damuwarki, na yi miki alkawarin sai inda karfina ya kare wajen sama miki farin ciki, don ke amana ce a hannuna fiye da wannan yaron, kuma amanar ce tsakanina da ke, ki gaya min ko mene ne Fahimah ta. Fahima ta riga ta kudire a zuciyarta sai dai ciwon son Uwais ya yi ajalinta, amma ba za ta taba furta hakan ga kowa ba balle mahaifiya a gare shi. Idan ta tursasa shi ya aure ta to ta kai shi ina? Mutum gashinan kamar malaikan daukar rai wane dadi mace za ta ji a aurensa? Macen ma wadda ya fi tsana fiye da kowa a duniya? Don haka ta soma tunanin abin da za ta fada wa Ammi ba tare da ta sanya mata kokonto ba. Abubuwa da yawa na damunta, not only UWAIS SHAGARI. Tana son sanin asalinta, tana son sanin su waye suka yi sanadin zuwanta duniya. Ammi ba ta son tambayar nan ko kankani, amma yau dole da ita za ta bi ta kare kanta da mutuncinta a idanun Ammi Safiyyah. Ammi, babu ciwo mafi muni ga dan Adam irin a ce ba ya da asali, bai san su waye suka haife shi ba, bai san shi dan sunnah ne ko shege ba. Ammi ko ba ki fada ba na dade da ganewa, orphanage da muke zuwa shi ne gidanmu, shi ne asali da tushe na, a can ki ka dauko ni. Ta karasa cikin wani irin kuka da ya keta har cikin zuciyar Hajiya Safiyyah. A yau ita kanta Ammi ta rasa da kalaman da za ta lallashi Fahimah, ta fahimci irin ciwon da ta ke ji a ranta, kuma ba ta isa ta warkar mata da shi ba. Kama ta ta yi ta rungume a jikinta ta ce, Fahima, in kin yarda ni ma UWA ce, sannan kokarina ya kai na kowacce UWA, to ki dubi Allah ki cire wannan damuwar daga ranki. Im your mother, father and Uwais is your brother. Ki sani babu wanda rayuwa ta ke cikakka a gare shi, babu kuma wanda Ubangiji ba ya jarraba in one way or the other. Mumini an sanshi da karbar kaddarar Ubangiji da kasancewa cikin godiyarsa ala kulli halin. Wannan damuwar da ki ka sanya kanki babu abin da za ta janyo sai nakasu ga lafiyar zuciya da kwakwalwar ki. Insha Allah wata mai kamawa za mu je Umrah mu yi ibada mu nemi kusanci da Ubangiji, za ki samu sukunin zuciyarki insha Allahu. Haka Ammi ta yi ta lallashin Fahimah, da kalamai masu dadi da nuna kauna har sai da ta sanya murmushi a kan fatar bakinta. ****** 9/23/21, 8:15 PM - Buhainat: Kafin muryarsan nan mai tada tsigogin jikinta ta biyo baya. A yau har wani kauri ta kara mai nuna ya zama cikakken mutum. Wanda ya gama mallakar duk abinda da Da namiji ke bukata a rayuwar sa. Ta juya a hankali ta dube su da fararen idanunta suna shigowa, hannun su cikin na juna sun yi balain dacewa da juna, kyau na bugun kyau. Ko hasidin iza hassada ya kalle su sai ya yaba su a ransa. Wani abu wai perfect match. Da gaske KISHI gaskiya ne a tare da kowacce diya mace, kuma Fahimah ta ji shi a kirjinta har fiye da misali, yau ga ta ga matar Uwais! Wadda ta dade tana kimanta zuwan ranar haduwar su da juna, amma murmushin da Amrah ta yi mata da innocence looks dinta sun sanya Fahimah mayar mata da martanin murmushinta. Ta kuma amsa sallamarta. Sannan ta maida kai ga abinda take yi bata kara kallon su ba. Uwais kamar ya fashe don bakin ciki don bai so Amrah ta ganta ba shiyasa ya kawo ta da safe, lokacin da ya tabbata tana barci. Bayan sun wuce falon zuwa falo na gaba Amrah ta juya tana kallonsa da sigar da ta ke kallonsa, wadda ta bambanta da yadda ta ke kallon kowa, ta ce, Ina ku ka samo kyakkyawar budurwa haka? Ba ka taba gaya min kana da sister ba. Cikin harshen Turanci ta yi maganar. Fahimah daga inda ta ke tsaye tana jiyo shi yana bai wa matarshi amsa da cewa, Mai aikin Ammi ce. Suka wuce turakar Ammi, Amrah na waiwayonta tana ta mata murmushi, sai ta samu kanta da kasa maida mata martani sakamakon zuciyarta ta yi bakikkirin da jin amsar da Uwais ya bayar a kanta. Daga bisani ta yi murmushi mai ciwo, cikin ranta ta ce, ban da abun ki Fahimah, don Uwais ya ce ke yar aikin gidansu ce ai ya kara miki matsayi, tunda bai ce da matarsa tsinto ki suka yi a gidan marayu ba. Maganar a ce ita matarsa ce ma ba ta taso ba. Ta ci gaba da daukar aure a tsakaninsu a matsayin shifcin gizo, zai fi mata sauki; wato irin almarar nan mai zuwa ta wuce wa dan adam yadda kowacce almara ke zuwa ta wuce, haka aurenta da Uwais zai zo ya wuce ba tare da ya zama actual reality ba. A hankali ta zame jiki daga wurin zuwa dakinta tana cewa cikin ranta, ina ma ita ce Amrah? Watakila da ita ce ke da kyan da Amrah ke da shi da Uwais ya so ta. Ta yi maza ta kwabi zuciyarta a kan hakan. Shes proud of her own beauty no matter what, watakila ko da ta fi duk matan duniya kyau asalinta ma kadai ya isa ya sa Uwais ya kyamace ta. Don haka Fahimah ta soma kallon aurenta da Uwais a matsayin dabaibayi rather than defensive kamar yadda Ammi Safeeyah ke kallonsa. Anya kuwa tunani da tsinkayen Ammi a kansu daidai ne? Ta yi ta zama da igiyar auren Uwais a kanta kenan don kawai a kira ta matarsa? Anya auren bai zame mata dabaibayi ba ya hana ta yancinta na yammatanci? Ko da ta ke yar gidan marayu in da Ammi ta yi hakuri ba za ta rasa me sonta a duniya ba, ko ta auri orphan dan uwanta a gidan marayun, soyayyar da zuciyarta ke yi wa Uwais da ma mai zaman kanta ce. Da Ammi ta yi hakuri ba ta yi amfani da karfin ikonta na uwa ba wajen ganin Uwais ya aure ta ba, da sannu za ta iya overcoming dinta (rinjayarta). Haka ta yi ta saka da warwara ita kadai a daki tanajuyejuye akan gado, idan ta ce ta yi watsi da alamarin Uwais, idan tsautsayi ya gifta suka hadu ko yaya ne, tofa dole sai zuciyarta ta motsa. Daga nan ta gane cewa soyayyar gaskiya abu ce da zuciya ba za ta iya kaucewa ba. Saidai ayi mata pretending. Amma daga yau da Uwais ya gaya wa matarsa ita yar aikin gidansu ce, daga yau za ta soma yaki da duk wata soyayyar UWAIS daga zuciyarta, ko da kuwa da karfin addu'ah ne. ****** Amrah ba ta samu wata special reception daga Ammi ba, daga gaisuwa shi ke nan, ta ce, In ce ko ba matsala? Amrah ta ce, Babu Ammi. To Allah ya yi muku albarka. Daga haka ta shiga wata hidimar a daki. Ta dai fahimci Amrah za a zauna lafiya da ita daga dukkan alamu, bata da kwaramniya kuma bata da girman kai ba kamar sauran yayan masu kudi irinta ba, shes very simple a cikin muamalarta da kowa. Tunda suka dauko hanyar komawa gida, Amrah ke zubo wa Uwais tambayoyi duk kuma a kan Fahimah, shi kuwa komai ta tambaya cewa yake bai sani ba. Yadda ta ga yarinyar shi ma haka ya ganta a gidan. Amma wallahi Habib-Qalby ba ta yi kama da yan aiki ba. Zubinta irin na matan kasar Sirreleone irin kalar fatarta nake burin ina ma in samu. I hate so much brightness. Ga dasashin cikin bakin ta irin wanda nake shaawa, da a ce ni mazauniya ce da na roki Ammi ta bar min ita, I just like the girl. Uwais dai sai "umh" yake cewa, yana ci gaba da tukin motarsa cikin nutsuwa har suka isa gida. Sun yi shirin kwanciya ya shigo dakin Amrah da zummar yin wani abu, sai ya ganta tana kora magani a bakinta. Da sauri ya idasa shigowa dakin zuwa gabanta. Lafiya Amrah? Ba ki da lafiya ne? Ta ce, No, lafiyata kalau. Contraceptive pills ne nake hadiya sabida su aka min recommending kan cewa sun fi rashin illah ga wanda bai taba haihuwa ba. Tunda Uwais ya hadu da Amrah daga dating (soyayya) zuwa aurensu ba su taba samun sabani ba, bai taba jin haushinta a ransa ko miskala zarratin ba. Amma yau ya ce, Amrah! Cikin kakkausar murya. Zan amince da komai, karatu a Malaysia, amma ban da a dinga zubar min da kwayayen haihuwata. Ban sani ba ko iya su Allah ya yi nufin ba ni a duniya. Amrah ta dube shi tana kankance idanu, Habib-Qalby, me ka ke nufi ne? Ina MBBS student in haihu yanzu? Kwata-kwata nawa nake? Ko shekaru ashirin ban rufa ba, ni karatuna ya fi min komai muhimmanci, wallahi... Uwais ya yi mata wani irin kallo, ya ce, Har da ni Amrah? Ai da abuna ka gan ni ka aure ni, ban ga dalilin da zai kai ni haihuwa yanzu ba. Uwais ya yi sake da baki yana kallonta. Rana ta farko da ya soma tunanin anya nan gaba zai iya tankwara Amrah? Yayi sake tun farko. Anya bai yi kuskure ba da ya nuna wa Amrah matsananciyar soyayya a fili? Juyawa ya yi ba tare da ya ce komai ba, zuciyarsa na tafarfasa. Ba abin da yake so a duniya irin haihuwa, kasancewar shi daya tal! Allah ya bai wa mahaifiyarsa. Yayan da yake burin haifa su yake fatan su zamo masa yan uwa. Ashe Amrah rariya ta ke kora su. Don haka kwanaki biyu da suka biyo baya ya dauke wa Amrah wuta, amarci da soyayya sun tsaya, wanda hakan ya jefa Amrah a damuwa. Amma abinda yake so da ita ba mai yiwuwa ba ne. Ya za ta yi da Da alhalin tana karatu a wata uwa duniya? Sai yanzu ya fahimci cewa, ashe dai duk son da yake wa Amrah har gobe yana nan a Uwaisunsa. Murmushinsa duk ya tsaya, haka yawan sakewar da yake wa Amrah. Damuwar da Amrah ta shiga ba ta misaltuwa, musamman da yake Uwais ya koyar da ita wata irin soyayya mai wuyar bari, yanzu ya dawo ya koma tamkar ba shi ba, ita kuma ba za ta iya bin raayinsa ba. Aunty Murjanatu ta kira domin neman shawara tana kuka, Uwais have changed completely, haihuwa yake so Aunty Murja, ni kuma ban shirya ba. Ya kasa fahimtata, akalla ina bukatar shekaru biyar nan gaba kafin na amince na fara haihuwa. Murja ta ce, Amrah in kina son kwanciyar hankali a gidan aurenki ki bi abin da mijinki ke so, tun ba ki yi sanadin da dimbin soyayyar da yake miki za ta ragu ba. Komai na Allah ne, ke ba ki isa ki tsarawa kanki rayuwa ba sai abin da Ubangiji ya tsara miki, haihuwa ba ta hana komai sai ki dauki Nanny. Da haka Murjanatu ta samu ta rarrashi Amrah ta kuma tabbatar mata a daren yau za ta je ta bai wa Uwais hakuri. Shiri na musamman Amrah ta yi zuwa dakin Uwais cikin wasu tausasan nighties. Uwais na loosing tie din wuyansa bayan ya dawo aiki bai ji motsin shigowar Amrah ba, sai ji ya yi ta rungume shi ta baya, kamshin sassanyan turarenta Yves Saint Laurent da sulbin hannunta su suka gaya masa ita ce. Ya lumshe ido yana tuno wahalar da ya sha a kwanakin nan da ya hora kansa da rashin Amrah. Zai iya cewa shi ne horo mafi muni da ya taba karba a rayuwar sa bayan horon auren Fahimah wanda sanadin auren Amrah ya ja masa, amma ya fiye masa a kan ya biye wa abin da Amrah ke so. Ko Ammi ta ji za ta kara tsanarta ne a kara lika masa wannan abun aman (Fahima). Shi kuwa da wani abu makamancin auratayya ya shiga tsakaninsa da Fahimah gara ya koma mace (ya yi losing manhood dinsa). Im sorry Habeeb-Qalby, something like this will not happen again I surrender. Murmushi ya yi, ya janyo ta ta dawo gabansa, wani irin kissing dinta ya shiga yi, passionately, ya ce, Amrah in ki ka ba ni Da, kin gama min komai a rayuwa, ni ko ba za ki shayar da shi ba ki haifa ki ba ni abina, zan bai wa Ammi na ta kula min da shi. Amma in ki ka ce sai kin zama likita za ki haihu Amrah ai zuwa lokacin na soma furfura ina neman abokin tafiya masallaci ne. Zan taya ki raino ke har nakudar in ba ki so na yarda ki yi epidural. Ni dai burina in haihu da ke Amrah ko sau daya ne a rayuwa sabida son da nake miki. Yatsunta ta kai ta toshe masa baki, Na amince Habib-Qalby, Im now ready to conceive, kuma tare za mu raini dan mu ko yarmu insha Allahu, zan raba lokacina biyu in ba ku rabi, ka taya ni addua Allah ya ba ni kafadar dauka... Da sauri Uwais ya ce, Lah yukallifullahu nafsan illa wusaha. Maana, Allah ba ya dora wa wata rai face abin da za ta iya. Ke mace ce Amrah, kuma mace da aure da haihuwa a ka santa, don ita jaruma ce fiye da namiji, boko shi ne last priority hidimar aure tana kan gaba da komai. Amrah don ita ce hanyar shiga aljannah. Daga haka Uwais ya canza akalar hirar zuwa mafi aala a gare shi. Sumbutarta yake kusfa-kusfa kamar zai hadiye ta. Ya yi kewar Amrah a kwanaki uku kacal yadda biro ya yi kadan ya bayyana, haka ita ma sai da ta ji idanunta sun cika da hawaye don tausayin Uwais, domin ta lura ba karamin azabtar da shi ta yi ba. Addua ta ke, Allah ya ba ta lafiya da tsawon ran da za ta ci gaba da kulawa da bukatar gangar jikin Uwais da lafiyar haifa masa yaya, ta yarda Uwais mai sonta ne, mai kuma matukar kaunarta wanda ya bambanta da sauran maza a halayya da dabi'a wajen nuna wa matansu soyayya a fili, abinda maza da yawa basa iyawa a wannan zamanin sabida girman kai. Alhaji Umar Dikko ya raini yayansa ne da tarbiyya ta ilmin boko zallah don haka ya;yan gidansu duka sun fi fifita boko a kan komai. Abin da Uwais ya lura da shi ke nan da ya sa yake ta yi wa Amrah uzuri a bisa sababbn dabiun da yake ta gani a tare da ita, wadanda suka sabawa nashi upbringing din. Alal misali, Amrah ba ta canza daga irin shigarta ta baya ba, wadda ta ke yi kafin aure ta dan kankanin gyale, hira da abokan karatunta maza, ta waya duk sanda take so, girki ma kuma ba kullum ta ke yi ba yanzu, in kuma ta yin, to sau daya a rana, sannan kuma very simple wanda ta tabbatar ba zai wuce mata minti goma ba, haka Uwais yake hakuri da abubuwa da dama bayan wadannan wadanda yake ganin sun sha bamban da na gidan da ya fito. Su ma yan boko ne, amma ba masu dabiun nasara ba. Uwarsa is an Associate Professor. Amrah ko a ina ta ke za ta iya bude lemo ta sha a tsaye haka yanayin dressing dinta ba ka iya bambance shi da na budurwa mara aure. Wani abun ko ya gyara mata in bai yi daidai da raayin gidansu ba, ba za ta yi ba. A wurin Uwais duka wannan mai sauki ne tunda yana samun yadda yake so da Amrah a shimfida. A wannan fannin kam yana yaba mata, kuma yana samun contentment don haka duk wani flaws na Amrah kankani ne a idanun sa. Hausawa suka ce, so hana ganin aibi, shi Uwais bayan son da yake wa Amrah har da kauna yar usli mara algus. Ya kama nan da kwana uku Amrah za ta koma Malaysia, bayan sun shafe watanni ukku tare suna barzar amarci, don haka Uwais yau duk a dame yake, ya zama upset ya kasa nutsuwa a ofis. Kusan duk bayan mintuna talatin sai ya kira Amrah a waya don ji yake kamar kafin ya kima gida zai je ya tarar ta koma Malaysia. Sai yanzu da ya san dadin aure ya fahimci cewa yayi babban kuskure da ya yarda da yarjejeniyar karatun Amrah, lokacin idanun sa sun rufe da neman aure, bai yi tunani consequences ba, yanzu kam ya fahimci bai iya rayuwa shikadai na tsayin sati biyu ma ba watanni hudu ba babu mace, in hakan ta faru akwai babbbar matsala, wadda bai san yaya zai yi da ita ba.. Duk da kasancewar sa matashi mai jini a jika, mai tashen kuruciya da hatiman banki, Ubangiji Allah bai dora masa sha'awar zina ba, bai taba fatanta wa kansa ba don haka ya shiga tunanin mafita ga rayuwar sa. Don ba zai bar Halal ya sabawa Ubangiji don karatun Amrah ba. Don haka yau da ya taso aiki shine sayi banza sayi hopi duk da yasan Amrah na so na makulashe da kayan amfani saida ya biya ya sayo mata. Ya san abinda ya tarkowa kansa ba karami bane amma an ce faduwar gaba asarar namiji, kuma a ganin sa a halin yanzu ai yafi Alhaji Umar Dikko iko da Amrah. Amrah tun daga kofar falo ta tare shi, ta ci sassanyar kwalliyar ta mai taba ruhin Uwais, bakaken riga da wando ne a jikin ta samfurin CK, ta makalkale cikin jikin sa kamar zata yi kuka "Habib-Qalby, yau ka dade baka dawo ba, saura kadan in bi bayanka, ga duhu ya fara shigowa ka sanni da tsoro". Makale ta yayi a kafadun sa suka karasa bedroom din su yana fadin " i'm sorry Amrah, na je nemo miki pizza dinnan ne da kike so ta Dominos, na tarar basu bude ba sai da naje wani wajen mai nisa" ya fada yana bude ledojin da yayo mata sayayyar, sai smiling take yi gashi duk abubuwan da take so ne. Uwais ya gama sanin Amrah ciki da bai, ta manna masa kyakkyawar sumba a kunci sannan tace "nagode Habiby, amma tare zamu ci, i'll be chewing it for you (zan dinga tauna maka)". Dariya Uwais yayi ya marairaice ido tamkar yaron dake gaban Mamarsa "a hakan kuma da dukkan zuciyar ki murna kike zaki tafi ki barni ni daya. Anya Amrah ba zamu sake shawara ba? Nace me zai hana tunda bakiyi nisa da fara karatun nan ba a shekarar farko kike ki hakura, na nema miki admission a BUK, Ammi na acan take bazaki sha wahalar samun admission ba. A ganina Amrah kasancewar mu tare yafi komai muhimmanci, mu shirya welcoming our incoming babies...... Amrah i'm sorry na yi alkawarin da na zo ina tantamar yiwuwar sa, i can't live without a wife Amrah, bansan irin ragaitacciyar rayuwar da zan yi ba. In kin amince Daddy ba zai ce komai ba tunda rayuwar mu ce mu biyu ba tasu ba.....". 9/23/21, 8:15 PM - Buhainat: Idanun Amrah har wani kanakancewa suka shiga yi sabida bacin rai, tace "Habiby, ka san abinda kake fada kuwa? BUK? Who? Ni Amran? Amran da na sani Amrah Umar Dikko? In ma wasa kake tun wuri ka bari kafin Daddy ya ji ka". Ta mike cikin fushi ba tare da ta dauki komai daga sayayyar da ya yi mata ba ta nufi dakin ta. Tana shiga daki mahaifin ta ta kira, tana kuka ta gaya masa duk abinda Uwais ya ce. Alh. Umar Dikko murmushi yayi irin na manya da suka san halin dan adam. Yace. "Ke ba tantabara sarkin soyayya ba? Duk Yayyen ki wacece tayi aure kafin ta ci karfin karatun ta sai ke? Kin ga farar fata kin rude kin yarda da dadin bakin sa. Abinda baki sani ba mu maza duk halin mu daya bama iya rayuwa babu mace. Kafin ya aure ki ba abinda bazai ce ba, amma yanzu tunda kin zama nama sai yadda yayi dake. Tun farko ma me ya kai ki kula shi har kika bari soyayya ta shiga tsakanin ku kina level 1? Inda kin bi tsarin dana yi miki tun farko da hakan bata faru ba. Amma tunda bisa yarjejeniyar nan muka amince aka yi auren ni da iyayen sa to yayi kadan wallahi. Gobe zan turo direba kawai ki biyo shi ku taho, daga nan Abuja ki wuce Malaysia, in zai iya auren ya jira ki as promised, in bazai iya ba babu dole fa a rayuwar nan Amrah... your future is your life, kafin kiyi tunanin farin cikin namiji think of your future, think of yourself first, kafin kowa ya biyo baya. Your husband only wants to destroy your future......" Amrah bata iya ta karasa sauraron abinda Daddyn ta ke fadi akan Uwais ba ta kashe wayar ta. Ta san Uwais yana son ta, kuma son ne yasa yake son kasancewa da ita, amma is it true that he wants to destroy her future?? Tambayar da bazata iya yiwa Uwais ba, domin yanada kima a idanunta da madaukakiyar daraja, saidai bazata yarda ta bari ya kassara burin rayuwar ta ba don amfanin kansa. Yau ma kowa a dakin sa ya kwana. Everyone of them is entitled to his opinion. Uwais ya tafi aiki a washegari ba tare da Amrah ta bashi karin kumallo ba kuma batare da ya ganta ba. Wajejen karfe biyu na rana yana fama da ayyuka a kwamfutar ofishinsa sakon Amrah ya shigo masa. "On my way to Abuja, daga can zan wuce Malaysia, See you soon... so much Love. -Amrah. Al'amarin da ya daurewa Uwais kai, ya kasa koda motsi akan kujerar sa. Bai taba hango matsala kwatankwacin wannan zata kasance tsakanin sa da Amrah ba. In yayi la'akari da cewa auren so da kauna suka yi dukkannin su. Amma Amrah har zata iya yanke wannan hukuncin ga auren sa ba tare da ta ji ko dar ba? Lokaci na farko da ya ji yayi fushi matsananci da Amrah, fushi kuma ba na wasa ba. Ya sa a ransa zai daure ba zai kara neman ta ba ko a waya har sai ya ga iya gudun ruwan su ita da mahaifin ta. Don tsananin bacin rai da ya koma gida sai ya samu kansa da janyo trollies yana hada kayan sa, gara masa ya koma gidan Ammi da ya zauna gwauro har tsayin wata hudu. Ko ba komai zai dinga samun abinci. Amma yau da wata ce ta yi masa haka ba Amrah ba, zai hakura da auren ta ne kawai. Amma Amrah zata ci alfarmomi har guda biyu; alfarmar son da yake mata da kuma mutuncin dake tsakanin sa da Jabeer. Ammi na falo tana karatun 'Bulugul Maram' din ta. Sanye da shudiyar laffaya, da butar shayin ta da tambulan a gefe, sai ganin maigadi tayi yayai sallama yana shigowa da akwatunan Uwais, yana wucewa da su part din sa. Ta saki baki tana kallon sa a lokacin da yake shigowa. Fuskar nan tayi jawur, ta nan take gane fushin Uwais ko bacin ransa tun yana yaro. Bata ce komai ba har ya zo ya samu wuri ya zauna daga gefen kafafun ta. "Ammi masa'ul khair" Tana cigaba da kallon sa ta amsa fuskar ta ba yabo ba fallasa, sannan tace "wadannan akwatunan fa? Ko balaguro zaka yi?" Ya girgiza kai cikin shanye bacin rai, don ya san Ammi ba wai tana farin ciki da auren sa da Amrah bane kawai ba yadda zata yi ne kuma tana so ta bashi hakkin sa, shi yasa ta yarda ya aure ta. Don haka dole ya rufawa Amrah asiri don dorar da dangantakar su. Yace. "Babu komai Ammi. Amrah ta koma makaranta ne, sai bayan watannni hudu zata samu hutu, shiyasa na dawo gida kawai don kadaici zai dame ni, babbar matsala ta abinci". Ammi cikin mamaki tace "makaranta a ina?" "Limkokwing, Malaysia" Ammi ta rasa abinda zata ce, daga bisani ta ce "dama ka san tana karatu a wata kasar ka aure ta? Ko kuwa sabon zance ne?" Uwais ya sunkuyar da kai, sai yanzu yake ganin wautar kansa, sannan yace "eh Ammi" sai kawai ta gyada kai ta ce "Allah ya bada nasara". Har wata ajiyar zuciya Uwais ya saki don bai zaci Ammi zata gajarta zancen a haka ba. Shi kuma baya son zancen yayi tsaho har ya kai ga fada mata cewa Amrah ta tafi ne ba tare da iznin sa ba. Haj. Safeeyah tace "bari in sa Fahimah ta gyara maka dakin, don tun bayan tafiyar ka babu wanda yayi amfani da sassan, na san yayi kura sosai, Talatu bata nan na aiketa kasuwa". Ba tareda ta saurari me zai ce ba tasa murya tana kiran FAHIMAH. Uwais sai ya sunkuyar da kai, sannan ya ji gaban sa ya fadi, da ya tuna wai itama zaman matar sa take. Zaman shi ta ke yi. Don shi sam ya manta da ita da existence din ta. Fahimah ta fito daga kicin dauke da madaidaicin tray data shiryowa kanta abinci zata ci, ta shigo falon tana amsa kiran Ammi ba tareda ta san Uwais yana nan ba. Dai-dai lokacin da Uwais ya dago kai. Sexy eyes din sa suka sauka akan Fahimah. Ita kuma bata tsammaci ganin sa a falon ba, don haka farantin dake hannnun ta da duk abinda ke kai ta saki a kasa ba tareda ta sani ba. Idanun Uwais na da matukar tasiri ga mental well-being din ta, ta yadda a duk lokacin da ya dubeta da su take neman hankalin ta da nutsuwarta ta rasa. Komai dake kan farantin ya kife, tangaran sun fashe sannan jikin ta ya hau bari. Ammi takaici ya ishe ta na yadda Fahimah bata iya mallakar kanta a duk lokacin da ta ga Uwais kamar wadda ta ga mala'ikan daukar rai, tace. "Yau nake ganin sakarci, sai ki dauko tsintsiya da mopper ki share, ke ba makauniya ba balle ace tuntube kika yi, kiyi maza ki kwashe kije ki gyara masa sassansa". Ta juya a sanyaye ta koma kicin don ta dauko tsintsiyar. Uwais mikewa yayi yana sakin dan karamin tsakin da Ammi bata ji ba. "Zan je wajen Jabeer na dawo Ammi, kafin a gyara dakin". Ammi tace "Rehlah Sa'eedah" wato a dawo lafiya. Bayan fitar sa Ammi ta bishi da kallo sannan ta yi murmushi ta maida duban ta ga Fahimah wadda ke durkushe tana tsaftace wurin data yi messing, ta kasa dagowa har Uwais ya zo ya wuce ta gaban ta. Ammi a ranta tace "muje zuwa dai, ai sannu - sannu bata hana zuwa ai, sai dai a dade ba'a je ba". ***** FAHIMAH A DAKIN UWAIS Wannan ne karo na farko data taba shigowa dakin Uwais a rayuwar ta, da farko kasa tabuka komai tayi, domin ji tayi gabadaya kuzarin jikin ta ya kare, koda yayi watanni baya dakin kamshin tsadadden turaren sa 'Maison Francis' bai bar sanyaya dakin ba. Babban hoton sa window size cikin kayan aikin sa na GT shi yafi daukar hankalin ta domin yayi kyau ba na wasa ba a cikin hoton. A jikin bed-side wani dan karamin hoton ne cikin frame da ya sha adon zuciya, fuskar sa ce data Amrah a ciki kamar zasu sumbaci juna. A hankali ta kai hannu ta dauki hoton a tafin hannun ta tana share kurar jikin sa da gefen gyalenta, tana kallon su da wani irin mixed feelings da ya fi kama da "kishi mai nukurkusa zuciya". Kishin da bata taba ji akan Amrah ba sai yau, ganin yadda ta maida Uwais jazur, ga 'yar kiba yayi, tabbacin yana samun gamsashshiyar soyayyar mace. Mai mace kamar Amrah yaushe zai taba waiwayar ta? Amma me? Mayaudariyar zuciyar ta sai ta ci gaba da bata hope da courage na cewa wata rana irin haka na zuwa....ranar da zata ga fuskarta haka gab da ta Uwais, watakila closeness din har ya fi haka. Duk da haka bata jin kin Amrah a ranta domin ta yaba da yadda ta karbeta a ganin ta na farko da ita. Ba abunda ke bukatar gyara a dakin sai kura da ko'ina yayi, don haka ta hau karkade komai tana gogewa tayi shara ta gyara abinda duk ya kamata ta tsaftace, sannan ta wanke masa toilet wanda yake fari kal shi ko kurar ma bai yi ba fari kal yake tabbacin a baya yana samun kulawa sosai. Da ta kammala ta feshe dakin da 'air freshner' din 'raspberry' ta shimfida masa sabon bedsheet mai kauri da Ammi ta bata ta shigo da shi sannan ta juya zata fita. Kamar wadda aka yiwa umarni sai ta sake juyowa, ta kalli hoton sa dake kafe, sannan ta runtse idon ta ta juya ta fita. "Na gama Ammi!" Ta fadawa Haj. Safeeyah dake zaune tana lazumi, mace ce mai yawan ibadah da bata bari lokacinta ya wuce a banza. Kai ta gyada mata. Sai Fahimah ta wuce kitchen ta tadda Baba Talatu don ta taya ta shirya abincin Uwais. Ko dama can tare suke girkin su muddin Fahimah tana gida. Suna cikin aikin Baba Talatu ta dube ta sosai ta ga kullum kara ramewa take yi. Ta san dole Fahimah ta kasance cikin damuwa sai dai ta boye hakan a ranta, don bata taba ji ko ganin Aure irin nata ba. Har yau ta kasa gane manufar Ammi ta hada wannan baudadden aure, ita Fahimahn tana nan a gefe kusa da uwar sa, shi yana can tare da matar da yake so suna more kuruciyar su. Anya ko Fahimah bata son Uwais hakan bazai ke damun ta a karkashin zuciya ba? Koda yake Ammi tace jami'a zata fara, ta san Fahimar su da son karatu, watakil in ta fara zuwa makarantar zata samu abin debe kewa. Baba Talatu ta nisa ta ce. "Uwar daki na, daga yau ke kadai zaki dinga dafa abincin ubandaki na, sannan ke zaki dinga kai masa, gyaran dakin sa da kula da komai nasa a gidannan ya dawo wuyanki domin da ke yafi dacewa har zuwa lokacin da zai bar gidannan". Fahimah tayi mata kallon "sannu sarkin kankanba". Sannnan ta ce "shin Baba Talatu meye gami na da shi din?" Dariya Talatu tayi tace "wai ai naga aikin neman lada ne da neman aljannah, kiyi don neman dacewa da aljannah ba don komai ba" da sauri Fahimah ta girgiza kai "ban iya shishshigi ba, kuma bazan fara yanzu ba. Ayyukan neman lada yawa gare su. In ya ga dama ya bi matar sa. Ni ki daina alaqanta ni da Ya Uwais, don babu komai tsakanin mu bayan 'yan uwantakar musulinci da Ammi ta hada, kuma ita nake fatan ta cigaba da wanzuwa a tsakanin mu har karshen rayuwa ta. Baba Talatu ta yi murmushi ta ce "Fahimah har yanzu ke yarinya ce, amma yaya zaki nade hannu a kirji ki koma gefe ki barwa kishiya miji? Miji fa aka ce Fahimah ba saurayi ba! Ai kowanne li'irabi kike dashi ki ajiye shi a gefe ki yi hobbasar kwatarwa kanki 'YANCI don tabbatar da martabarki ta diya mace. Ni ban yarda wai wannan farar tsadar ta fi ki komai ba, mace sunan ta mace, kowacce irin kala ce ita, bahaushiya, balarabiya, ba'abziniya, bafullatana ke har bayerabiya duk daya muke. Balle ma Fahimah ke kike ganin kan ki a baya don baki da hasken fata irin ta ubandaki na, amma bakar mace ai ita ce mace ta alfarma, shi kansa ya san hakan sai don dai wani dalili nasa na daban amma.....". Zancen duk ya gundiri Fahimah, tace "Baba Talatu chapter closed, inda aka san darajar ka acan ne zaka yi rawa a baka kudi, a inda ba'a san darajarka ba kuwa maimakon ka samu kudi, kana iya karewa da dan banzan duka!". Uwais da ya je bai samu Jabeer a gida ba sai Murjanatu, ta gaya masa Jabeer yana Abuja, zurfin ciki irin na Uwais yasa bai tattauna komai akan matsalar sa da Amrah da Aunty Murjanatu ba duk da ya san kusancin dake tsakanin su. Maimakon ya koma gida sai ya samu gefen hanya ya gangara ya tsaya, ya kashe motar gabadaya yana kallon wayar sa da kiran Amrah ke ta shigowa akai-akai ba kakkautawa. Zuciyar soyayyah na azalzalarsa da ya dauka.....zuciyar maza na hambarewa. Duk son da yake yi wa Amrah dole ta yi abinda zai nuna mata shi ba irin mazan da mace ke juyawa bane don kawai yana son ta. Ya fi karfin mintuna ashirin a wurin yana tunanin abinda zai yiwa Amrah ya rama bacin ran data sanyashi, kin amsa kiranta is not enough. Amma ga mamakin sa ya kasa daukar wani matakin bayan wannan. Amrah ta riga ta yiwa zuciyar sa illah bai da wani katabus a kanta. Da kyar ya jawo motar ya dawo gida, bai tadda kowa a falon ba duk sun shige daka, ya wuce dakin sa kansa tsaye. Wani irin gyara da dakin ya samu da sanyin air fresh da Fahimah ta fesa su suka yi masa sallama, wadanda suka cakude da rabar iyakwandishan. Sai lokacin ya tuna ya ji sanda Ammi ke fadin Fahimah ta zo ta gyara masa daki. Tsaki yayi yana fadin "da abinda tafi dacewa kenan ai (aikatau) ba matar masu gida ba". 9/23/21, 8:15 PM - Buhainat: Washegari da safe Fahimah ta shirya masa breakfast, sabida Talatu ta yi sammako zuwa kauyen su Jahun 'yar ta ta haihu. Kunun gyada tayi masa fari kal mai gardi sai kosan dankalin turawa da ruwan shayin da ya zamewa al'ummar gidan duka farillah. Ya fito cikin casual - dress din sa na suit din ma'aikatan bankin GT misalin karfe bakwai dai-dai na safe. One thing shine baya wasa da cikin sa sabida fadin kirjin sa (physique) da motsa jiki da yake yi da Asubah yasa baya iya fita ba tare da ya karya ba. A jikin dining din ya sameta tana jera abincin, rigar barci ce a jikin ta da 'yar hula a kanta ta dora zanin atampa a saman rigar. Yana zuwa ya ja kujera ya zauna, ba tareda ya dubeta ba. Juyawa tayi ta bar wurin jin zata sake yin barin tangaranm ita kuma tayi alkawarin ta daina bada kanta gaban Uwais. Yayi tsammanin zata gaishe shi ne ya baiwa banza ajiyar ta. Ga madaukakin mamakin sa sai ta juya zuwa dakin ta ba tareda ta ko kalle shi ba. "Kin rufawa kan ki asiri". Ya fada yana tsiyaya kunun a kofi. Ko daga kyan kunun a ido ya tabbatar zai yi gardi a baki. "Kin taimaki mijin ki na gaba (idan Uwais ya sake ki) da kika tsaya kika iya girki. Don zaman Ammi kike yi ba nawa ba. Banda abun Ammi wannan Blakin ai sai ta dinga firgita mutum cikin dare. Gara da ta rike abar ta a gefen ta bata yi gigin kawo masa ita gida ba. La-shakkah da Amrah ta samu Kuku. Don bazai taba bude baki ya iya cewa Amrah yana da wata macen a duniya bayan ita ba. Bai yaudari Amrah ba, don da gaske har cikin zuciyar sa bai da wata mace bayan ita. Sama-sama ya ci abincin ya wuce dakin Ammi, tana zaune bisa darduma tana azkar din ta na safiya. "Na fito Ammi, sai na dawo. Sabahul khair". Daga masa kai ta yi ya juya ya fita. **** Yau Fahimah zata fara registration, don haka tare suka tafi da Ammi, kuma fannin da Ammi ke koyarwa shi ta zabar mata, don tace a fannin ne kawai zata iya dinga taimaka mata a gida wato tsimi da tanadi (economics). Kasancewar yanzu abu ake na sanayya, Fahimah bata sha wahalar samun gurbi fannin na tsimi da tanadi ba kamar sauran dalibai, duk da wahalar da yakeyi, tunda tana da uwa a gindin murhu. Da taimakon Ammi ta fara registration, kullum da safe tare suke tafiya, yau da suka fito akan titin su na komawa gida Ammi ta ce "Fahimah, is high time ki fara koyon tukin mota don ki dinga taimaka min kina taimakon kanki, tunda Surajo ya tsufa baya iya gani sosai, yanzu kuma ke matar aure ce, bai kamata ga mijin ki zaune a gida in dauko wani kato ya dinga kai ki makaranta ba, nikuma ba kullum nake shiga Campus ba, tafiyar mu zata saba in kika fara daukar lacca". Fahimah ta ce "Ammi to waye zai koya mini?" "Ni dai kin san bani da lokaci, tunda an shiga sabon semester, amma zan wa Uwais magana ya dinga koya miki a karshen mako". Ammi ta kirkiro zancen koyon mota ne don ta samar da kusanci ko yaya tsakanin Uwais da Fahimah don ta ga abin nasu ba mai alamar karewa bane. Kada kuma auren ya lalace a haka. Lokacin da Ammi ta furta masa wannan umarnin, fuskar Uwais komawa ta yi kamar hadarin da ya nausa yayi gabas. "In koya mata mota fa kika ce Ammi?" "Eh, abinda nace kenan" bai san sanda ya ce "Ammi muharramata ce?" Don shi shaf! Ya mance da wata Fahimah balle auren ta dake kansa. Ammi dunkule yatsunta tayi ta mika masa "ungo nan (dakuwa). A'ah ba muharramar ka bace, kanwar tsohon ka dake kabari ce". "Yau sabida Fahimah har Baban shi an zaga". Tashi yayi fuuuu! Ya wuce dakin sa. Abincin ma ya fasa ci. Ammi tana kai shi bango da yawa akan Fahimah yana hakuri ne kawai don UWA ta fi gaban wasa ammma da tuni Fahimah ta dade da komawa orphanage. Washegari Ammi ta samu waya daga babban dan Kawu Shuraim wato Mahdi, cikin kuka mai tsanani Mahdi yace. "Allah ya yi wa Abbu rasuwa yau din nan". "Innalilllahi wainna ilaihi rajioun". Ammi Safeeyah ta fada tana karawa. Ashe shiyasa ya dage ya zo ya yi wa Uwais aure? Ashe sallama ce ya yi musu, ashe rabuwar kenan, ashe daga wannan lokacin Uwais yayi rashin Kawun sa mai son sa da kaunar sa... Allahu akbar! Muryar Ammi kadai ya ji ya tabbatar kuka take yi. Uwais a zaune yake akan kujerar sa amma bai san sanda ya mike tsaye ba makale da wayar a kunnuwan sa, kansa ya kama ya dafe da hannayensa biyu a lokacin da Ammi ta fada masa rasuwar Kawu Shuraim. Babu irin kokarin da bai yi ba don ya samu excuse daga Banki ya bi Ammi Sudan amma bai samu ba, domin already yana daga cikin manyan ma'aikatan GT da zasu halarci seminar ta organization din nasu gabadaya, wadda suke yi duk karshen shekara a babban reshen su da ke jihar Lagos, zasu tafi cikin satinnan kuma an riga an mika sunan sa. Ammi ta so tafiya da Fahimah, amma ga nata karatun da bai gama nuna ba, kuma tana so ta jima a Khartoum wannan karon kasancewar ta dade bata je ba. Don haka dole ta bar ta a gida. Da daddare bayan Uwais ya dawo take tambayar sa "yaya ka samu excuse din ne zamu tafi tare ko yaya?" Ya kalli Ammi da tausayin ganin yadda mutuwar dan uwan ta ta buge ta, ta fyadar da ita a wuni guda, Ammi har ramewa ta yi. Idanun ta sun yi jazur sabida kuka. Ya ce a hankali "ban samu ba Ammi, don an tura ni cikin masu tafi seminar a Lagos nan da kwana uku, zan yi kwanaki ukku, sai dai idan na dawo, zan yi matukar kokari na samu adduar bakwai". Ammi ta ce yaushene tafiya Lagos din? Yace jibi Juma'ah, zamu dawo Lahadi don mu samu ofis litinin, sai in yi kokari a bar ni in zo Sudan ko na kwana biyune kacal". Ammi ta ce "to Yaya za'a yi da Fahimah? Don ni zan yi akalla sati biyu kuma tana zuwa makaranta, ga Talatu bata dawo ba har yau, don haka tunda Juma'ah, Asabar da Lahadi ne ka tafi tare da ita Lagos din, bazan barta ita kadai a gidannan ba. In kuka dawo ka samu izni daga ofis din sai ku taho Sudan tare ku samu addu'ar bakwai ku dawo tare, tunda dukkan ku kuna da passport na kasar Sudan". Wani gumi ne ya shiga barkowa Uwais daga kowacce kafa mai tsatstsafar da gumi ta jikin sa. Bai san san da ya kira sunan Ammi da hanzari ba. "AMMI!" Tune din muryar kamar na wanda zai fashe da kuka. "Muharrama ta ce da zan tafi da ita wani gari har kwanaki?" Ammi bata san sanda ta kai masa bugu da filon hannun ta ba, ta ce "idan ka sake yi min wannan tambayar ta rainin hankali wai ko Fahimah muharramarka ce sai na sassaba maka kamanni. A'a ba muharramarka bace, karuwa ce nace ka dauka ka tafi da ita. Kuma ka kula da marainiyar Allah Uwais, cin ta, shan ta da walwalarta. In ka ci amanata kai da Allah". Uwais ya mike yana rangaji ya bar falon, bakin ciki kamar ya hadiye zuciyar sa. Wai me ke damun Ammi ne? Idan da yana tunanin Dimentia ne yanzu kam ya tabbatar lafiya kalau take, tana matukar son hada rayuwar sa da yarinyar nan, yarinyar data riga tasan ita kadai take son abarta. Ya dauketa ya shiga da ita cikin abokan aikin sa ma ya ce matar sa ce ai ya sayowa kansa raini a wurin ta da wurin su. Wannan matar leburori ce da marassa gata ba irin tashi bace. Shi fa ba abunda bai so ma a duniya irin ganin black fuskarta, balle yasa ta a gefensa yana yawo da ita cikin Nigeria wai har ma da wajen ta (Sudan). Idan Amrah ta samu labari fa cewa he is with another woman me zata dauke shi? Hakan bai zama yaudara da cin amanar soyayyah ba? Zuciyar sa ta tambaya. Sannan ba tare da bata lokaci ba daya zuciyar ta halarto da amsa... Bai zama cin amana ba, tunda itama ka biya sadakin ta, matsalar tun farko bai kamata ka boyewa Amrah ba. In har tana son ka zata baka goyon ne baya kayi biyayya ga mahaifiyar ka. Yadda zuciyar sa zata iya jure hada muhalli da Fahimah a bakon wuri inda basu san kowa ba har na tsayin wasu kwanaki shine babbar damuwa a gare shi. **** Ya cigaba da yiwa Ammi shirin tafiya Sudan a yinin ranar duk da cewa he's frustrated amma bazaka taba ganin hakan akan fuskarsa ba, yana da charisma na boye fushi, ya saya mata tikiti, a lokaci guda yana nashi shirin na tafiya Lagos. Yayi waya da duka 'ya'yan Kawu Shuraim yayi musu ta'aziyyah musamman Mahdi, ya gaya musu uzurin sa na rashin biyo Ammi. A yau da daddare Ammi zata tashi, tun jiya Fahimah ta hada mata kayan da zata bukata a babbar jakar matafiya, bata san me ke faruwa tsakanin Ammi da Uwais akan ta ba. Karfe shidda na yamma Ammi ta shigo dakin ta, ta zauna dab da ita, sannan tace. "Fahimah, ban miki bayani ba tun jiya, na bari sai yau da zan tafi, ki hada kayan ki kamar kala shidda, idan na tafi yau, ku kuma gobe da safe zaku tashi zuwa Ikko". "Ni da wa Ammi.. wa muka sani a Lagos?" "Ke da mijin ki zaku tafi, ko akwai damuwa ne a cikin hakan?" Ta yi mata tambayar tana mai tsatstsareta da ido, don kada ta bata damar cewa komai. Fahimah ta ji miyan bakin ta ya kafe, ta fiddo idanuwa kawai zuruuu! Tana kallon Ammi. Wani abu ya shiga kan Ammi da alama. Ammi ta fahimci kallon da take mata sarai don haka tayi murmushi ta ce. "Kalle ni da kyau ki kara, lafiya ta sumul-kalau, a kullum ina addu'ar Allah ya kawo sanadin da shakuwa ko yaya zata shiga tsakanin ki da Uwais. Wannan nesa-nesan da kuke da juna shi yake bada babbar gudunmuwa wajen nesanta zukatanku da juna. Na baku lokaci, ban zaci abin naku zai kai haka ba, amma na fahimci in za'a shekara a haka zaku zauna har auren ya lalace. Ban ce lallai sai kun zauna gida daya ba, ni in dai zaku amsa sunan miji da mata ko a gidannan ne kiyi ta zama Fahimah, ki haifa min jikoki masu irin tarbiyyar ki, masu kama da ku, wadanda ni Allah bai bani da yawa ba. Uwais in dai irin halittar marigayi mahaifin sa gare shi, wallahi bai iya tsallake wannan tarkon dana dana masa. Ina nufin (bai iya yin kwanaki masu yawa babu mace). Don haka wuyar ta ku fahimci juna shike nan ina tabbatar miki komai zai wuce kamar ba'a yi shi ba. Sai tattali da soyayya da zasu biyo baya. Soyayya zata yi kanta a zukatanku duk da yanzun ma bani da tabbacin kiyayya ce kuke wa juna. In ma kiyayyar ce sai dai daga Uwais amma banda ke Fahimah. Na ga soyayya mai yawa cikin kwarar idanun ki....shiyasa ma na jajirce na hada wannan auren, don idan mace na son namiji, to kuwa tabbas zata yi hakuri da shi duk rintsi, ta rike shi matsayin uban 'ya'yan ta albarkacin wannan so da ta ke masa. Don haka bisa umarni na Fahimah, tashi ki hada kayan ki ki bi mijin ki zuwa inda duk yasa kafa wajen neman abincin sa. Allah yayi muku albarka". Fahimah bata ce komai ba, abinda bata son yi agaban Ammi shi ya zo (tears). Ammi da kanta ta shiga zabo mata kayan da ya kamata ta dauka daga cikin na lefen ta da aka dinko. Hatta kayan shafa dana kwalliya duk a acikin na lefen ta ta diba mata, ta hada mata su a matsakaiciyar trolley. Fahimah sai bin ta take da jikakkun ido har ta gama. Ta dube ta tana daga zaune a bakin gado duk jikin ta ya mutu. Ta yi kamar bata gane halin data ke ciki ba na zullumi da anxiousness. "In da abinda kike bukata na amfanin ki sai ki kara, na gaya miki kwana uku zaku yi, kuma in kun dawo da kwana biyu zaku biyo ni Sudan. Bakin Fahimah sai motsi yake tana so ta tambayi Ammi. "Shin Yaya Uwais ya amince da wannan tsarin nata?" Amma ta kasa furtawa har Ammi ta bar dakin. Ba abinda ta kara kan kayan da Ammi ta hada mata sai inner wears, sannan ta dauki pad, kasancewar tasan ta kusa yin period. Ita da Uwais din ne suka raka Ammi airport, karfe takwas na dare, kasancewar boarding flight zata bi. Suna can har karfe goma Uwais na shige da fice da kayan da Ammi zata tafi dasu gun (screening) kafin lokacin tashin su yayi. Gab da zasu tashi ya iso inda suke zaune itada Fahimah akan kujerun silver, yace. "Everything is set Ammi, Allah ya kiyaye hanya, safe journey". Ammi ta daga ido ta dube shi da murmushi, daidai lokacin da aka soma kiran pasinjan Sudan da su shiga jirgi. "Ina fatan kafin in dawo, komai zai zama tarihi Uwais. I mean tsakanin ka da Fahimah. Za ka rungumi auren ka da hannu bubbiyu, ka yarda Fahimah amanar Allah ce a hannun mu Uwais. Idan kana ganin takurawa ce na yi maka kayi hakuri ka bani dama, just give it a try, ni na haifeka Uwais don haka ka yarda bazan cutar da kai ba, komai na yi maka sai dai ya zamo taimako da soyayya. Kai da kanka watarana zaka zo kana gaya mini WACECE FAHIMAH? Wadanne irin baiwarwaki Allah yayi mata nayi maka wannan alkawarin. Kyal-kyal banza ya daina diban ka. Halin mutum shine abinda yake sawa a so shi ba nasaba ko zubin halitta ba... Above all this black da kake cewa is but expensive beauty, but only ta BRAVE MEN Uwais......". Ta karasa da murmushi, sannan ta mike tsaye don kowa ya shige ya barta, "I'm hoping that my son to be among them". Sannan ta kama hannun Fahimah wadda kanta ke sunkuye tana hawaye, ta sanya cikin tattausan hannun Uwais. Ta dunkule su ta cure wuri guda, sannan ta dauki hand bag dinta ta wuce zuwa terminal. Ya dade yana kalon bayan Ammi, sannan ya sauke ido akan hannun Fahimah dake dunkule cikin nasa, wadda tunda ta sunkuyar da kai hawaye take zubarwa bata dago ba. Ji take kamar ta bi Ammi, kamar Ammi sallama take musu, kamar in ta tafi ta bar su su kenan bazata dawo ba! Ta barta da miskilallen dan ta a inda bata da kowa. Kalaman Ammi Safeeyah sun luguiguita zuciyarta; wai namiji akewa wannan rokon akan ya so ta ita wace irin mara sa'a ce a rayuwar ta? Ta shiga ittikafin adadin soyayyar da Ammi ke mata....wadda duk itace silar hakan. Ko don wannan kauna da soyayya na Ammi Safeeyah, ta ci alwashin zama karkashin igiyoyin auren Uwais no matter what, sannan against all odds, ko da zai dinga zaftarar naman jikin ta ne kullum yana sawa a miya saboda kiyayya. Mu karasa a littafi na 2. 9/23/21, 8:15 PM - Buhainat: A daidai wannan lokacin Amrah na can cikin Aunties dinta ana yi mata kwalliya. Kasa daga kiran ta yi da ta ga sunansa ke yawo a screen din, domin Amrah yarinya ce mai alkunya. Aunty Murjanatu ta ce, Amrah ba kiranki ake bane?" Aunty Wasila ta ce, "Maybe angon ne ake jin kunyarmu". Ita dai ba ta tanka su ba har wayar ta katse. Yau ji ta ke ba wanda ta ke jin nauyi duk duniya irin Uwais. Aunty Wasila ta ce, "Amrah a haka za ki kama mijin? Yo yanzu wa yake kunyar amsa wayar mijinsa a ko ina? Zauna nan kina fulako, matan waje su kwace, wannan mijin naki wanke hannu ka taba". Duk aka yi dariya har make up artist din dake yi mata kwalliya. Still Amrah ta kasa daga wayar Uwais duk da sai kira yake har sau uku. Daga karshe ya turo text. Shi ma sai da ta saci idon su Aunty Murja sannan ta karanta. "Finally Mrs. Shagari. May this moment mark the beginning of the series of our blessings... May Allah's rahma cover us forever. I promised you eternal love Amrah and all the happiness that love can bring... I love you Amrah!" Uwais Shagari. Amrah ta yi catching numfashinta a hankali tana satar kallon yayyanta ko da wanda ya gane yadda sakon Uwais ya tafiyar da numfashinta na wucin gadi? Dukkansu hankalinsu ba ya kanta yana kan hirar dinner da za a yi yau da daddare. Ta yi ajiyar zuciya tana tunanin da idanun da za ta iya kara duban Uwais a sabon matsayinsa na miji a gare ta. Amrah na son Uwais, amma soyayyar Uwais ta fi ta Amrah yawa. Probably za ta iya ci gaba da rayuwarta normally ko babu Uwais ko da akwai shi. Yayin da Uwais zazzafar soyayya yake yi wa Amrah ta yadda rayuwarsa ba za ta taba cika babu Amrah ba. A can gidan Ammi yau ne wuni, don haka duk abokan arzikin Ammi sun zo, ciki har da Hajiya Asabe shugabar gidan marayu. Hajiya Asabe ta kwance jakarta ta soma fiddo 'yan kulle-kullen da ta zo da su tana yi wa Ammi bayani, kasancewar 'yar Sokoto ce ita, ta ce ita ga gudunmawarta kenan kayan gyaran amarya. Ammi ta karba ne kawai ta yi godiya, amma ta saka a ranta ba za ta bai wa Fahima komai ta ci ba. Matar da hankalin mijin ba ya kanta sam-sam za'a bai wa maganin mata ya sa ta ciwon mara a banza. Fahimah ba ta san ta zama matar Uwais ba, da halin da ta samu kanta a ciki yau, da jin cewa bikin Uwais ake yi da ba ta shige shi ba. Daga ita sai ubangijinta suka san cewa tana gab da zarewa. Wani dan karamin zaucewa ne ya same ta a daki sai safa da marwa ta ke a cikin dakinta tana magana ita kadai. "Yaya Uwais ya yi aure, zai tafi ya barmu... Matarsa mai sa'a ce... Ni ba ni da sa'a... Sai koshin wahala. In ya tafi gidansa shi ke nan na daina ganinsa... Ganinsa kawai is a blessing because it heals... Allah ka ba ni juriya, Allah ka ba ni dangana. Allah ka fahimtar da zuciyata ta daina son abin da ba za ta taba samu ba...". Sai ji ta yi ana bubbuga mata kofa da karfi. Muryar Ammi ce ke kiran sunanta, "Fahimah! Fahimah! Fito ku yi sallama da su Kawu Shuraim za su tashi yanzu zuwa Sudan". Ta soma kokarin regaining consciousness dinta don tabbas Ammi ta ganta a wannan halin ba abin da zai hana ta gano ta... Ta zama zararriya a kan dan ta Uwais, kishinsa na neman hallaka ta. Toilet ta fada da gudu ta wanke fuskarta da sabulu ta sanya hijab sannan ta fito, ta bi bayan Ammi zuwa falo. Duka kawunnin Uwais suka bi ta da kallo har ta samu gefen Ammi ta zauna. Ta gaishe su, muryarta ba ta fita sosai sabida kukan da ta ci. Baffa Haruna ya hau yi mata nasihar da ba ta san dalilinta ba, yana fadin ta zauna lafiya da abokiyar zamanta su ba wa mijinsu hadin kan da zai iya adalci a tsakaninsu. Ta dauki kishiyarta 'yar uwa ba kishiya ba, ta rike girmanta da Allah ya ba ta. Fahimah dai ba ta dago ba har zuwa lokacin da Kawu Shuraim ya ce, "Ki yi hakuri da dan uwanki Uwais, kin san ba da son ransa aka yi aurenku ba. Wannan burin na mahaifiyarsa ne, don haka tabbas sai kin yi hakuri Fahimah a zamanki tare da Uwais. Don Uwais wani baudadden mutum ne wanda idan aka yi gabas shi sai ya yi yamma, in aka yi kudu shi sai ya yi arewa. Hakurin shi ne kadai maslaha har zuwa sanda Allah zai daidaita ku, don haka ba za mu gaji da cewa ki yi hakuri ba kin ji ko Fahimah?" A hankali Fahimah ta dago rinannun idanunta ta sauke a kan Ammi Safeeyyah. So ta ke ta tantance ma'anar kalaman da ke fita daga bakunan kawunnan Uwais, shin ko idanun Ammi za su ba ta assurance na abin da dattijan nan ke cewa? A zahiri cikinsu babu sa'anta, babu abokin wasanta balle ta yi zaton wasa ne irin na kaka da jika suke yi mata. Ammi ta gyada mata kai a hankali tana murmushi da ba ta tabbaci daga fararen kwayan idanunta. "Uwargidan Uwais!". In ji Ammi tana mai sanya tattausan hannunta cikin na Fahimah. "Allah ya ba ku zaman lafiya. Da zuri'a mai albarka. Allah ya kade fitina da dukkan abun ki". Fahima sai ta samu kanta cikin wani hali na 'fita hayyaci' na wucin gadi. Ta nemi jinta da ganinta na 'yan dakikai ta rasa. Don haka har su Baffa suka yi sallama da Ammi suka fita Fahimah ba ta koma cikin hayyacinta ba. Watakila dai mafarki ta ke yi... Irin mafarkin da dan Adam ke yi idan ya cika sanya tunanin abu a ransa. Mafarkin kasancewa matar Uwais ai ba yau ta fara ba. Don haka na yau din ma in ta yi hakuri za ta farka ne kada ta yaudari kanta. Har sai da Ammi ta raka su Baffa ta dawo Fahimah na nan kafe a inda Ammi ta barta, rokon Allah ta ke yi a zuci ya yi gaggawar farkar da ita daga wannan rudadden mafarki. Ammi na shigowa ta kama hannunta ta cira ta tsaye suka nufi dakin barcinta. A gefen gadonta ta zaunar da Fahima wadda zuwa yanzu ta fara ji a jikinta yau ba mafarki ta ke ba, wani babban alamari ke shirin faruwa da ita, wanda ba za ta ce alkhairi ba ne. Idan kalamansu gaskiya ne sun aura mata Uwais shin hakan zai haifar da Da mai ido a gare ta? Wanda ba ya sonka fa bai sonka har abada, kuma ba zai taba sonka ba balle an hada auren da na matar da yake so, ai kawai in hakan ya tabbata ta amince kawai karshen Fahimah ya zo (the end of FAHIMAH). Don dai ta san Uwais ba zai barta da rai da numfashi ba, ba zai barta ta shaki numfashi a matsayin matarsa ba, balle su hada inuwa daya, inuwar ma wadda ta fi kowacce alfarma wato inuwar aure. Maimakon farin ciki duk da mayataccen son da zuciyar Fahimah ke yi wa Uwais, ji ta yi wani irin tsoro da firgici ya mamaye ta, kada Allah ya nuna mata ranar da za ta kara haduwa da Yaya Uwais ko da a hanya ne. Kamar yadda suka ce burin na Ammi ne, ta yadda Ammi za ta yi mata kauna fin haka. Ji ta yi hawaye sun jika fuskarta sharkaf ba tare da ta ankara ba, Ammi gorar ruwa ta dauko a firji mai sanyi ta zubo a tambulan ta mika wa Fahimah, ganin yadda ta ke yanka gumi daga zaune kamar wadda ke dakin nakuda duk da rabar iyakwandishan da ta lullube dakin Ammin. Kusa da ita Ammi ta zauna, ta ce, kuka Fahimah? Ki yi hakuri in na miki ba daidai ba, ban iya rabuwa da ke Fahimah zuwa gidan wani, bansan irin kalubalen da zaki fuskanta ba, haka ba zan iya jurar ki wulakanta a gidan aure ba, a dalilin haka ne na yanke shawarar aura wa Uwais ke ba tare da neman shawara ko amincewar kowannenku ba don na san ba za ku taba amincewa ba bisa karan-kanku. Amma Allah shi ne shaidata kan cewa ALHERI nake nufinku da shi, ba za ku gane hakan ba ku duka sai ranar da bana raye. A yanzu dai ba hadin kanku nake nema ba don abin da nake nema na same shi, burina ya cika. Fahimah kin dauwama cikin zuriata. Dukkanku kuna bukatar lokaci kafin ku tantance aya da tsakuwa, ki kwantar da hankalinki in dai a kan Uwais ne ba zan kai ki gidansa ba sai bisa amincewar zukatanku ku duka. Ki je ki hada kayanki na sati biyu, gobe insha Allah in an kai masa amaryarsa ni da ke za mu tashi zuwa umrah, ba za mu dawo ba sai bayan sati biyu. Jiki a mace Fahimah ta mike amma ta kasa ce da Ammi komai. Idan na yi miki ba daidai ba, idan hukunci na bai miki daidai ba ki yi hakuri ki yafe min Fahimah. Da sauri Fahimah ta juyo, tausayin Ammi wadda tsufa ya soma bayyana a gare ta duk sai ya kamata. Cikin rishin kuka ta ce, Ammi, ba ki yi min komai ba. Sannan ta sa kai zuwa dakinta. Burinta a rayuwa komai ya girmansa a yau ya cika. Mafarkanta sun zamo gaskiya, ta zamo wani bangare na Uwais Shagari, amma abin mamaki ta kasa farin ciki da hakan, watakila don girman kalubalen da ta ke hangowa ne, watakila kuma don ta san auren ba zabin Uwais ba ne, in ma ya sani ke nan. Jin kanta ta ke tamkar wadda ta rako dukkan mata duniya sabida rashin saarta a rayuwa. Gabadaya maganar auren da auren kansa ba ta san a ajin da ya dace ta sanya su ba. Da me za ta ji ne a rayuwarta? Maraici, rashin asali and finally BORANCI? Kodayake Ammi ta ce ba kai ta gidan Uwais za ta yi ba, sai ranar da dukkansu suka amincewa hakan. Ranar da ta tabbata ba mai zuwa ba ce, sai dai ta dauwama da sunan matar Uwais, amma auren ba zai taba zama reality ba. Yadda Fahimah ta ga rana haka ta ga dare a wannan ranar, kitsawa ta ke tana tufkewa sannan ta warware. Ta rasa makomar rayuwarta. A karshe ta sa a ranta cewa, ya kamata ta yarda cewa, duk bakinta da Uwais ke fadi yana gorantawa ita ma mace ce kamar sauran mata, wadda wani namijin bayan Uwais zai iya gani ya ce yana so ya biya sadaki ya dauka ya kai gidansa. In haka ne kenan ya kamata ta martaba kanta....Ta daina kallon kanta wulakantacciya. Ba kuma ta kowacce hanya ba face ta yin gefe da UWAIS daga zuciyarta, shi da duk abin da ya shafe shi. Ta maida komai nasa a bakomai ba, ta maida hankali kadai ga karatun da Ammi ke so ta yi, ta gina wa kanta future yadda duk ranar da babu Ammi za ta tsaya da kafafunta. Ta dauki aurenta da Uwais a matsayin shifcin gizo in ba haka ba ita ce a wahale. Ta tsaya ta nema wa kanta madafa ga rayuwarta ta gaba, wanda ba komai ba ne san yin ilmi da zai ba ta martabar da kyawun halitta ba ya badawa. Kyawun halittar da ta fi tunanin a kansa ne Uwais bai sonta. "Goddam Black" kamar yadda yake cewa tana alfahari da bakin fatarta. Ammi ta sha gaya mata Black is beauty a duk lokacin da Yaya Uwais ya ce mata Black, kuma babu mummuna sam a yaya mata sai wadda ba ta martaba kanta ba. Da kyar barci ya sace fahimah a wannan daren cike da tunanin da ta kwanta da shi. ****** Washegari Ammi da Fahimah suka tashi Umrah zuwa kasa mai tsarki. Ammi ta yi haka ne don ta nesanta Fahimah da Uwais na dan lokaci, ya kuma samu lokaci da matar sonsa yadda ya kamata. Duk adduar Ammi a Harami da Masjid Nabawy a kan Uwais da Fahimah ne, ita kadai ta san adadin abubuwan alkhairin da ta ke roka musu. A can Kano, ango da amarya suna ta barzar amarci babu kama hannun yaro. Uwais ya matukar jin dadin tafiyar Ammi da Fahimah, don ba ya so ko da kuskure a samu wanda zai gaya wa Amrah yana da wata matar bayan ita. Alhaji Umar Dikko ya zuba dukiya a gidan Amrah kamar bai san zafin nema ba. Gidansu komai ya yi acan-acan, soyayya ruwan zuma gangariya tsakanin Uwais da Amrah ba su taba gundura da juna. Kafin Ammi da Fahimah su dawo Saudiyyah ango da amarya har wata yar kiba suka hada a kumatunansu sabida kwanciyar hankali da samun contentment in life. Ranar asabar da daddare suka sauka a filin jirgin saman Malam Aminu Kano. Fahimah ta yi wa kanta sayayya sosai, haka ta yi wa Talatu tsaraba. Ba yadda Ammi ba ta yi da ita ba a kan ta yi wa Uwais tsaraba ko ta carbi ne, Fahimah ta ki. Yadda ta yi fatali da Uwais daga zuciyarta haka ta ke fatan ta manta da ko sunansa. Dan halak din shi ya zo daukarsu zuwa gida, ya sha excelcior fara kal, sai walainiya ya ke. Da ganin shi ka ga angon daje kan ganiyar sa. Motarshi kamar a nan ne kamfanin Maison Francis yake. Ga wani farin gilashin PRADA da ya manna ma dogon karan hancinsa. Kallo daya da Fahimah ta yi masa ba ta kara maimaitawa ba, duk da kuwa cewa zuciyarta ta yi mugun raurawa. Sakamakon wata irin ilhama da kamala da aure ya kara wa Uwais, gara ita ta kalle shi sau daya, shi ko sau dayan bai kalle ta ba. Sai da ya mallaki Amrah ya kara gane babu wata sauran diya mace da za ta kara burge shi a duniya. Babban tashin hankalinsa a kwanakin nan shi ne in ya tuna Amrah tafiya za ta yi ta barshi shi kadai a gidansu, aikinsa kuma ba irin na yawo ba ne duk lokacin da aka ga dama. Ya soma da ya sanin alkawarinsa na barin Amrah ta ci gaba da karatu a jamiar Limkokwing, sai dai ya san bai isa ba, ya yi kadan, yayi tsararo ya daga wannan alkawarin daga muhallinsa. Amrah ta sangarta shi da abubuwa da yawa a sati uku kacal, ga iya girki, ga tsafta ga shagwaba sannan uwa-uba ta iya bi da shi a shimfida. Duk da karancin shekarunta. Suna tafe a kan hanyarsu ta zuwa gida daga airport tsakanin shi da Ammi kawai suke hira a motar, Fahimah tamkar ba ta gurin a motar, amma har cikin bargonta ta ke jin tasirin muryar Uwais har tsigar jikinta na tashi, suna isowa gida ko gama parking motar bai yi ba ta bude murfin motar ta yi cikin gida. Ta gilashin motarsa ya saci kallonta, sanye ta ke da jallabiya kirar Oman ruwan toka da mayafinsu. Kayan sun karbi choculate colour din jikinta sosai. Sannan ta yi dan haske irin na kamawar wanka a jikin mace mai tsafta. Uwais ya dauke kai daga dubanta yana sakin tsaki a ransa. Mace sai fadin ran tsiya kamar diyar qaruna, nan kuwa diyar kwalin taliyar indomie ce. Maigadi ya sauke akwatunansu zuwa ckin gida. Da gudu Talatu ta fito tana "oyoyo uwar dakina", ta rungume Fahima wadda ke ta murmushi don ita ba ta kyalkyala dariya sam, murmushi kawai ta ke wanda ke maida ita kamar furen fulawa idan ta yi shi sabida bakin dadashin cikin bakinta da ke bayyana a duk lokacin da ta yi murmushi. Da taimakon Talatu suka kimtsa duk kayan da suka dawo da su a muhallinsu bayan Fahimah ta ware mata tsarabarta. Fahimah ba ta san cewa Uwais ya gaya wa Ammi washegari zai kawo Amrah ta yi mata barka da zuwa ba. Gajiyar tafiya ya sa ta koma barci bayan sallar asubah, ba ta fito ba sai karfe goma na safe, ta yi wanka ta shirya cikin wasu riga da wando pakistan ruwan dorawa, ta kame kakkarfan gashin ta da ribbon kanta babu kallabi, tana tsaye jikin dining tana decorating wurin da kayan kawata dining area da ta sayo daga Saudiyyah ta ji sallamar mace. 9/23/21, 8:19 PM - Buhainat: A hanyarsu ta dawowa Uwais tuki kawai yake ba ya ko kwakkwaran motsi har suka iso gida. Yana yin parking Fahimah ta fice, har tana tuntube saura kadan ta fadi, Uwais ya bita da kallon takaici, dakinta ta shige ta murza key. Ta jingina bayan ta a jikin kofar tana sauke ajiyar zuciya mai nauyi. Me ke shirin faruwa ne da rayuwar ta a yau? Ammi na son actualizing wannan auren a lokacin da daga ita har shi Uwais din ba su shirya ba. A baya ta ce ne sai lokacin da suka shirya karbar juna a matsayin ma'aurata don kansu. Abinda su duka biyun suka tabbatar ba mai yiwuwa bane. Amma yau kwatsam! Ta shammaci kowannen su a lokacin da suka riga suka sakankance cewa auren na su ba mai tabbata bane sannan ba zai je ko nan da can ba. Yau Ammi ta dauko wata gagarumar rigima wadda baza'a ce rikicin tsufa yayi dalilin ta ba. Don kuwa bata yi tsufan da zata ce ta manta waye UWAIS ba? Kuma kuma yaya matsayin ita Fahimah yake a gare shi? Ta riga ta gama sakankancewa cewa auren ta da Uwais suna ne kawai, sannan a suna zai kare. Daga ranar da aka daura shi zuwa ranar da zai gaji da ajiyar sa ya bata takardar saki. Yau ina zata tsoma rayuwar ta idan ta bi Uwais zuwa inda bata san kowa ba? A gaban Ammi ma ya ta kare da shi balle a bayan idon ta, karkashin mulkin sa da ikon sa? Kawai sai ta ji hawaye na zubo mata. Hawayen ba na komai ba ne na tausayin kanta ne. Namiji sai ana rarrashin sa ana kalallamar sa ana nusar da shi a kan ya so ta! Don kawai bata da iyaye kamar kowa! Ko da ya ke watakila Uwais na kin ta sabida kalar fatar ta ne idan ta yi la'akari da irin kalaman da ke fita daga bakin sa akan ta duk lokacin da ya bushi iskar izzar sa. Ita wace irin mara sa’a ce a cikin mata? Kuma wace irin kaddara ke bibiyar ta? Daga maraici da rashin asali.... yanzu kuma zuwa BORANCI! A wannan lokacin wani irin determination (kudiri) ya kutso ya shigi zuciyar Fahimah Shagari.... Determination na self-defence and self-actualization; abin nufi ta tsaya ta san hakikanin kanta, ta kuma kare kanta daga farmakin zuciyarta akan Uwais; kada ta bari soyayyar Uwais dake dankare a zuciyarta ta kassara ta, ta zamo barrier ga farin-cikin ta da cigaban rayuwar ta, ta zubar da kimarta ta diya mace mai daraja a dalilin soyayya. Zata yi kokari iyakar yin ta, ta ga cewa ko ta ina aka je aka dawo ta baiwa Yaya Uwais mamaki sabani ga tunanin sa; she is not begging for his love. Hakannan komai nasa yanzu ya koma ba komai ba a idanunta (ya daina burgeta). Sannan duk yadda ta kai da son sa a baya, daga lokacin da aka sanar da ita an yi musu aure duk wani infatuation sai da ya kama gaban sa. Su ci gaba da zama a yadda suke a duk inda za su je ba damuwar ta ba ne matukar zata rike determination dinnan nata. Uwais ya rike duk abinda yake takama da shi itama daga yau ta koyi sarrafa kanta akan sa. Abinda Ammi ke fatan ya kasance insha Allah ba zai kasance ba, karewa ma ita yau ta fara period kuma sai ta yi kusan kwana hudu yake daukewa. Kuma an ce tafiyar ta kwanaki uku ce. Tunanin hakan da ta yi ya sa ta jin wani irin relief a zuciyarta. Ta bar bakin kofar zuwa toilet ta sakar wa kanta shower mai dumi kamar yadda ake a al’adarta kullum kafin ta kwanta barci. A duk lokacin da tayi hakan zata yi barci mai dadi ne har da saleba. To yau ma hakan. Domin kwata-kwata ta cire damuwar tafiyar daga ran ta. Sai sake-sake da kintace-kintacen abinda zai faru. Bayan sallahr asubah ta sake wanka ta shirya cikin koriyar atamparta vlisco, ba ta san takamai-mai karfe nawa za su tafi ba, don haka ta kishingide a kan gado da zummar kafin cikar karfe takwas na safe ta sake bincikawa in ma tafiya yayi ya barta ta sani, tayi abinda ke gabanta. Ai kuwa barci mai nauyi ya sadado ya yi awon gaba da ita. Don jiya tunani da sake-saken yadda tafiyar ta da Uwais zata kasance kadai bai barta ta yi barci yadda ya kamata ba. Can! Cikin barcinta ta ji ana buga mata kofa da dan karfi, kamar za'a jijjigeta. “Who is this?" Fahimah Ta tambaya cikin mamaki da mutstsike ido. Shiru ba amsa, tamkar da dutse take magana, nan jikin ta ya bata ko waye, saukowa ta yi daga gadon ta bude kofar don ganin wanda ke mata wannan bugun kamar ana binta bashi. Uwais ta gani harde da hannuwa a kirji sai huci yake kamar mesa, ya hade cikin jamfa da wando na wani tattausan voyel sky blue, as usual hular kansa ta nitse cikin tsakiyar sumar kansa. Wani kallo ya yi mata kamar fararen kwayar idanunsa za su fado don harara, sannan ya nuna mata agogon hannunsa. “Are you awareâ€? an lika min ke kuma zaki bata min lokaci ki ka shige daki kina ta barci? Me za mu ci kafin mu bar gida ko ni ki ke jira in je in girka miki?â€? Fahimah ta tsuke baki, sannan ta murguda shi gefe ta rabe ta gefensa ta wuce zuwa kitchen ba tare da ta tanka masa ba. Ya saki baki yana kallonta da madaukakin mamaki har ta shige kitchen, shi ta ke murguda wa baki? Girgiza kai ya yi ya bi ta kitchen din. Cikin hargagi yace. “You Goddam Black, 15 minutes na baki ki sama min abin da zan ci, bana hawa jirgi ban ci komai ba, cikina hautsinewa yake yiâ€?. Fahimah dai bata amsa ba, ta baiwa banza ajiyar sa, sai kokarin kunna heater din dafa ruwan zafi da ta ke yi. Da alama so yake ta tanka ya ji dadin bata mata rai, ya ci mutuncin ta a banza bata da mai tare mata, to ba za ta tanka shi ba. Don an ce karfe daya baya amo. “Irin ga dan iska din nan ko, ina magana kin bai wa banza ajiyata?â€? Fahimah ta ga in ba ta amsa ba zai iya yin zuciya ya shigo ya makure ta, ko ya samu ya huce haushin manna masa ita da Ammi ta yi, ga shi su biyu kacal a cikin gida babu mai ceton ta. Sai ta ga gara ta tanka, don ya san ta daina tsoronsa yanzu, kuma tana iya mallakar kanta a gabansa. Sannan ba zamansa take yi ba zaman Ammi take yi. “Don Allah ka sarara min mana! Kafin 15 minutes din ma zan kawoâ€?. Ta fada ciki-ciki kamar mai kunkuni. Babu tabbacin ya ji ta ko bai ji ta ba. Tsiwa take so tayi masa amma tana tsoro. Fatanta ya bar mata kicin din. Ko ta samu ta saita bugun zuciyar ta. Kada tayi abind ta saba yi a gaban sa. Tsayuwarsa a wurin na maida ita unease, jikinta ya ki sakewa ya yi aiki yadda ya kamata. Kamar wadda ke cikin sanyin kankara a dalilin kasancewar sa a wurin tare da ita. Daurewa kawai take yi don tsira da determination din ta akan Uwais Shagari. Amma ga mamakinta Uwais ya ki tafiya, karewa ma shigowa ya yi kitchen din ya haye kan island ya yi zamansa. So yake ya gargasa mata magana ko yaya ne kafin ya yarda ya dauketa su tafi, wadda har ta koma ga mahaliccinta ba za ta mance ba ya sonta ba. "Yanzu ke kin yarda Ammi ta rusa miki rayuwa da mijin da ba ya sonki, bai taba sonki ba, kuma ba zai taba sonki ba? Me ya sa ba ki yi wata hobbasa don kwatar wa kanki ‘yanci ba? Ba ki da masaniyar ina da mata ne, wadda nake matukar so kamar na ba ta raina?â€? Tunda ya fara maganar Fahimah ba ta dago ba, firar dankali ta ke, amma da ya zo sentence dinsa na karshe sai ji ta yi ta tafi da tsokar hannunta, wato ta yanke hannunta da kakkaifar wukar da ke hannunta. “Ina da matar da nake so, kamar na ba ta rainaâ€?. Wani statement ne wanda shi a wurinsa ba komai ba. Amma a gare ta tamkar digar ruwan dalma ne a kan fatar jikinta. Tana so ta ba shi amsa, daidai da wadda ta dace da munanan maganganunsa sai ta tuna UWAIS ne. Wani kwayan mutum guda daya da zuciya da ruhinta ke so, wanda ta yi wa kanta alkawarin zama da shi da kasancewa tare da shi against all odds koda zai yi ta yankar tsokar naman jikin ta yana sanyawa a miya albarkacin Ammi Safeeyyah - Basudaniyyah. Balle common bakar magana akan matar da yake so. Sai ta saki wukar da ke hannunta kasa, hade da dankalin ganin jini yana fita. Ta kudire ko dukanta Uwais zai yi cikin gidannan ba za ta soya masa dankalin nan ba, ko dai ya tafi da yunwarsa, ko ya kirawo matar da zai iya bai wa rai ta soya masa daga Malaysia. Ta kashe komai ta wuce ta gabansa hannun ta nan digar jini ba tare da ta ce da shi komai ba. Murmushin mugunta ya yi, ko ba komai ya ci nasara, ya yi spoiling mood dinta ita ga amarya zata bi miji Ikko, ta samu miji a bagas sabida ba Amrah, kuma gashi ya janyo ta yanke hannu. Sai yaji bai ji dadi ba daga kasan ransa saboda ko kadan ba ya son ganin jini ko yaya daga jikin dan Adam. Don haka ya sauya shawara ya bi bayanta zuwa dakinta ba tare da ta san ya biyo ta ba. Toilet ta shige ta sakar wa hannun famfo a sink, tana kalon jinin jikin ta na gudu treda ruwan tana hawaye, sai jin motsin mutum ta yi daga bayanta. Da sauri ta juya a tsorace, ashe har ya iso gab da ita sai da ta bigi kirjinsa. Da sauri ta ja baya. Dan farin bandeji ne a hannunsa na nade ciwo da ruwan hydrogen, daya dauko a dakin Ammi, sabida bata wasa da first aid ita, ba tare da ya ce komai ba ya kama yatsan ya zuba hydrogen a kan yankan, sannan ya soma kokarin daurewa da bandejin. Fahimah, ta kusa suma a wannan lokacin sabida kyakkyawan closeness din da ya shiga tsakanin ta da Uwais. Wanda hakan bai taba faruwa ba koda da kuskure. Ita da Uwais sai kallo daga nesa. Wani irin sassanyar kamshi yake yi na Maison Francis (Baccarat Rouge) dake tashi a hankali daga jikin sa. Shi kuwa Uwais bai yi don wata manufa ba, sai don tunawa da ya yi da kalaman Ammi. “Fahimah amanar Allah ce tsakaninmu Uwaisâ€? na ba ka amanartaâ€? idan ka cutar da ita kai da Allah…â€?. 9/23/21, 8:19 PM - Buhainat: Ita in wani ne ya gaya mata a baya cewa Uwais na magana haka ma, ba za ta taba yarda ba. He is not that miskili to such an extent kamar yadda ta dauka a baya, kawai dai magana sai ya ga damar yin ta, kuma in ya so yana yin abar sa sosai ko da bazaka bashi amsa ba. Uwais Shagari, ya fara sassauta wa ransa kiyayyar Fahima a bisa dalilai da dama..... Muhimmi shi ne, ganewa da ya yi ita din is a source of geniune happiness na mahaifiyar sa wadda in ya zauna da ita ko da ba ya kyautata mata in disguise Ammi za ta yi ta farin ciki da shi ne, tareda sanya masa albarka. Sannan auren su wani abu ne inevitable (wanda ba makawar sa) wanda bazai iya tsallakewa ba, watakila har abada, don ba zai taba iya mikawa Ammi takardar saki ko ta wata mace daban, balle wannan wadda take so kamar ita ta haifa ba. In haka ne kenan takurawa rai da kiyayyar da babu riba a cikin ta aikin banza ne. Zai zauna da Fahimah koda har abada ba zaya so ta ba. Sai ta zauna zaman Ladan Noma (as he called it). Tunda haka Ammi ta zaba mata. A kullum yana tuna dawainiyar da Ammi ta yi da shi tun yana yaro, da dawainiyar ilminsa a bayan ran mahaifinsa ba tare da taimakon kowa ba. Ita ke kaishi makaranta ta dauko shi tun daga primary har secondary bata yarda kowa yayi mata wannan aikin. Yau ga shi yana ta cin gajiyar ilmin ta ko’ina, sannan ta bar shi ya auri Amrah duk da yakinin da yake da shi na ba ta sonta, amma ta kwatanta adalci ko a fuska ba ta taba nunawa Amrah ko wani ba. Ammi na da wasu irin principles (doctrines) akan akan karan-kanta, wadanda ta dora Fahimah a kai, wanda su ne ta ke masa kwadayi, amma ya kasa ganewa da gangan. Yana can ga kyale-kyalen da baya lasting. Tana da tabbacin watarana zai gane din, tana raye ko bata raye, cewa Fahimah matar rufin asiri ce kuma babban alkhairi a gareshi, har ma ya zo ya gode mata da dukkan godiyar da zai iya. What he needs most is time ....and closeness ga Fahimah. Bayan fitarsa Fahimah ta ga ya dace ta sauya sutturar jikinta ko da ba ta yi kwalliyar da Ammi ke so ba, don haka ta yi wankanta a nitse, da Olay shower gel (goats' milk), ta fito ta zauna shafa, sannan ta fiddo wani jan material da aka yi wa fitted gown ta sanya, yana da ratsin golden da baki a jikinsa. Ta yi daurin kai ya zauna cif, sannan ta matsa gaban mudubi tana duba turarukan da Uwais ya ajiye a wajen har guda uku. Ashe sunan turaren Uwais ke nan (Maison Francis, Baccarat Rouge). Kwarai ta dade tana son kamshin, domin kuwa kamshinsa na mannewa a zuciya ne tamkar maganadisu, musamman ga ruhin diya mace ma'abociyar soyayyar da bata samu martani ba. Ba ta san lokacin da ta kai turaren ga bakinta ta sumbata ba, and it feels likeâ€?.. like Uwais din himself ta ji ta sumbata apparently. Wanda hakan ya aika wani irin sako cikin ruhinta, wanda ta ji shi tun daga kwakwalwa har zuwa toe wato babban yatsar kafar ta. Something like emotion mai narka zuciya, da sanya wani irin daddadan feeling..... Fahimah ta shiga waiwaye ko da wanda ya ga abun kunyar da ta yi (sumbatar turaren Uwais). Ga dukkan taimakon Allah, sai ya kasance babu kowa. Daga ita sai Ubangijin ta kadai, sune kuma kadai suka san adadin son da ta ke yi wa Uwais Shagari. Tana kuma rokonSa Azza Wa Jallah a kan in son da ta ke yi wa Uwais, ba alkhairi ba ne a gare ta to ya yaye mata bakidaya ko ya sassauta mata. Akuyar cikinta ta yi kukan da ke tuna mata rabonta da abinci tun jiya. And cikinta na da nasa hakkin a kanta ba soyayyar Uwais kadai ba. Wadda ta zamo mafi rinjayen abin da ke consuming lokacin ta. Idan ta lula a duniyar tunanin Uwais, ba ta sanin cewa lokaci na tafiya, sai ta farga da awannin da ta karar ba tare da ta san me ta ke yi ba. Hormones dinta suna da karfi, da ba su sabbaba mata ciwon tunani a kan Uwais ba. She then decided to prayâ€? wato ta yanke shawarar komawa ga addu'a akan Uwais Shagari, tunda an ce addu’a maganin komai ce. Addu'ar data dukufa yi a yau itace. Idan son da ta ke wa Uwais alkhairi ne, Allah ya juyo da hankalinsa kanta cikin gaggawa. Idan ba alkhairi ba ne a gare ta, Allah ya nesanta zuciyarta daga kansa Ya raba ta da wannan koshin wahala. Karfe biyu aka kawo mata abinci mai rai da motsi taci sama-sama daga nan kuma barci mai dadi ya dauke ta, barci sosai ta yi wanda ba ta farka ba har Uwais ya dawo. Karar sautin talabijin shi ya sanar da ita dawowarsa. Da ta bude ido ta dubi inda yake zaune yana shan lemun power horse daga shi sai farar singlet da dogon wandon suit din da ya cire. Jikinsa ne ya gaya masa tana kallon shi, ya juya ya sakar mata harara a ran shi yana fadin ta kafe shi da ido kamar mayya, ko sun hada jini da maitar ma wa ya sani ne? Kunya sosai ta ji da ya kama ta kane-kane a cikin kallonsa. “Are you not praying ne ke? (Ke ba kya sallah ne)? Tunda muka zo ban ga kin dungura goshinki gaban Ubangiji ba, sai kallon mazan mutane kamar kya cinye su?â€? Fahimah ta tsuke baki da fuska cikin bacin ran kalaman sa, sannan ta mike daga kwanciyar. Ya dan bi ta da kallo tana wucewa ta gabansa, sai ya ji kamshin turaren sa na tashi a jikin ta kadan-kadan. "Lallai ma yarinyar nan ta fara raina ni". Uwais ya fada a ransa. Amma bai furta mata ba dai in ma ta yi ne don ya tanka. Anyway jan kayan nan sun mata kyau as black as she is, sannan she’s tall, slim and well-structured. Bar ta dai da 'bakin ta' da ke munana ta (dark-skinned). But even her lips are looking luscious, succulent and irresitable to every tensed manâ€?" da sauri Uwais ya shafo sumar kansa cike da fargabar Allah ya sa ba a fili ya fadi wadannan baranbaramar kalaman ba. Daidai lokacin da ta fito daga toilet fuskarta da damshin ruwa, sai ya ga ruwan ba ya mannewa a kan fatarta sabida sulbinta. Sai digewa yake dis-dis. Da sauri ya kauda kansa da suka hada ido, yana tambayar kansa, me yake kallo ne haka??? Duhu ya shigo, bayan ya yi sallar isha ya ji yana da bukatar fita supermarket, akwai abubuwan bukata da yake son sayo musu. Ya mike ya maida rigar sa, ya dau wayarsa ya sa a aljihu ya durfafi kofa. Fahimah ta fahimci Uwais fita zai sake yi a daren nan, ba ta san lokacin da ta zari mayafinta ta rufa masa baya ba saura kadan su yi karo a bakin kofa. “Ke lafiya? Ina za ki haka?â€? Ai kawai ba ta san sanda ta rike gefen rigarsa ba. “Zan jira ka a waje ka je ka dawo, dazu bayan ka fita aka yi ta kwankwasa min kofa. Ni gaskiya tsoro nake ji an ce Lagos ana kidnappingâ€?. Ta fada da iyakar gaskiyarta. Uwais ya rasa me zai ce, sai ya kalli hannunta da ya rike masa riga gam! “To cika ni tukunna ko?â€? Ta sake shi cikin jin kunyar abin da ta yi, har ga Allah tsoro ta ji, ba ta san lokacin da ta yi hakan ba. Juyawa ya yi ya fita ta rufa masa baya, ya rufe kofar dakin. Suna sauka ta lifter yana kiran direbansu da ke zirga-zirga da su, don haka suka samu direban ya yi parking kofar reception yana jiransu. “Please take us to the nearest supermarketâ€?. “It’s done, Sir.â€? Tafiyar mintuna sha biyar suka yi ya kai su wani supermarket shahararre a nan Ikoyi. Fahimah ba ta yi niyyar fita ba, amma da ta tuna pad dinta saura uku sai kawai ta balle murfin mota ta bi shi a baya ba tare da ya sani ba. Shi dai sai hango ta ya yi a wani bangare daban na shagon tana daukar abu. Ya yi kamar bai ganta ba ya ci gaba da sayayyarsa. Duk abin da za su bukata da ma wanda ba za su bukata ba sai da ya daukar musu daga nan Lagos har zuwa Sudan. Ta ja gefe ta tsaya tana ta kallon mutane wadanda yawancinsu couples ne da yaransu suke sayayya gwanin sha’awa. Da ta ga ya doshi wajen biyan kudi, sai tayi maza ta bi shi a baya tana dan bobboye abin da ta dauko. Daga bayansa ta tsaya, ya yi kamar bai ganta ba. Da aka fara lissafa kayansa ya juya yana amsa waya, sai ta yi wuf! Ta jefa always pad din data dauko cikin kayan. Da ATM card ya biya aka dauko masa kayan zuwa mota. Suna shiga wayar Ammi na shigo masa. “Ka ce in ka koma gida za ka ba ni Fahimah kuma na ji shiruâ€?. “I’m sorry Ammi, mun dan fita ne zuwa supermarket, bari mu karasa masauki zan kira in ba taâ€?. “To lallai gobe ka duba lafiyar wayar ta, haka kawai Fahima ba ta kashe waya, gara da waya a kusa ko da ba ka nan za ta iya kiraâ€?. Suna ajewa direba ya ja motar. A can Khartoum Haj. Safeeyyah-Basudaniyyah sai ta dungura goshinta cikin hali na sujjadah ta godiya ga Ubangiji. Ko ma dai ya ya ne, ko ba shiri suke ba, ko ba soyayya suke ba, ko babu mu'amalar auratayya a tsakanin su, ta fahimci Uwais ya daina kin Fahimah, ya daina kyararta. Ya karbi auren ta kan ba yadda zai yi. Ya kuma fara daina dagawa kansa hankali akan kiyayyar ta. Shi yasa katin hannunsa ya bude dakin suka shige. Yana rufe kofar ya dube ta a dage, ya ce, “You Goddam Black, ina wayar ki? Your Mum wants to talk to you in bana nanâ€?. 9/23/21, 8:19 PM - Buhainat: Yana gama daure mata hannun ya fice ba tareda ya kalle ta ba, tare da cewa, “idan kin gama kukan I’m waiting for you outside. Ni ba ni nasa kika yanke ba balle ki kai karata wajen Mamar kiâ€?. Ta dauki mintuna biyar kafin ta iya komawa hayyacinta. Abubuwa na ta faruwa cikin ‘yan dakikannan kamar a mafarki. Kwakwalwarta ta kasa digesting kowanne daga ciki domin Uwais Shagari ya koma mata tamkar hawainiya. Bata yi zaton yana da wannan compassion din ko yaya a kanta ba, bata yi zaton zai yi wani action a dalilin fitar jini daga jikin ta ba. Har ya bita da kalaman kare kansa. Ta fahimci dai guilty ne ya lullubeshi kawai. Hijab dinta ta sanya wani zurmeme da shi sannan ta janyo trolley din kayanta ta da Ammi ta hada mata ta tadda shi a waje. Uwais ya baza shanyayyun lumsassun idanunsa don ganin ina Fahimah za ta zaba don zama. In ta jera da shi a gidan gaba ya zama raini, haka in ta je baya ta zauna ya zamanto shi ne direban ta ya zama rashin kunya da tsaurin ido, ace ya zama direban ‘yar gidan marayu tsintacciyar Ammi? Ga mamakinsa tsayawa ta yi hannayenta dogare da karfen trolley din tana jiran umarnin sa. Wato ya zaba mata wurin shiga da kan sa. "Bata da azarbabi" Ya fada calmly daga cikin motar ba tareda Fahimah ta ji shi ba. “To ai gara in zama direbanki da ki zauna a muhallin AMRAH, don haka shigo bayaâ€?. Ta kyabe baki ba tare da ya gane ba. Ta rasa me ya sa ta daina jin shakkar sa yanzu, ta fi alakanta hakan da maganganun da ya gargasa mata wadanda suka taimaka gaya wajen gaya mata ta kara martaba kanta a idanun Uwais idan shi bai martaba ta ba, ta daina yarda wata mace ta fi ta don kalar fata kamar yadda Baba Talatu ta ce. Sai dai kuma ba za ta iya yi masa tsaurin ido ba, don haka ne ta bi umarninsa ta bude booth ta sanya jakarta, sannan ta zagayo ta bude kofar baya ta shige kamar yadda ya umarta. Tana kallonsa sai da ya karanto addu’ar barin gida, ya shafa, sannan ya ja motar a nitse. Ya kure kira’ar Minshawy cikin suratul Nisa’i. Uwais na jin darajojin da Allah ya baiwa mata da hakkokin su a wurin Ubangiji kasancewar sa masanin tafsiri. Dukkansu zuciyarsu ta nutsu da sauraron karatun nan, tension din bacin-rai da fargaba da ke cikin zukatansu na tafiyarsu tare da juna da Ammi ta hada su ba zato ba tsammani ya ragu 50% a dalilin jin ayoyin Ubangiji mai girma. Ko da suka iso airport ya nemi inda ya adana motarsa kirar Elantra yadda ko kwana nawa ya yi zai dawo ya tadda ita a wajen lafiya. Fahimah dai bin Uwais ta ke inda duk ya jefa kafarsa kamar rakumi da akala, tana fama da jakarta da ta dan fi karfin ta domin ya ki karba mata tasa kawai yake ja. Ba su bata lokaci ba suka samu jirgin Bell-View mai tashi zuwa Ikko a yanzun nan. Uwais don dai ya bakanta wa Fahima sai ya kai ta economy class shi ya zauna a first class seats. Abin da bai sani ba Fahimah ko a jikin ta, don ba ta san wani bambanci tsakanin economy da first class ba. Ita hakan ma ya fi mata, domin zama kusa da Uwais ai ba karamin takura ba ne. Har suka sauka a Lagos ba ta bawa zuciyarta damar yin wani tunani ba bayan na yadda za ta zauna da Uwais a muhalli guda. Something inescapable, something terribleâ€?...something unavoidable, Ammi ta rigada ta hada tafiya kuma ta gudu ta bar ta, haka ta ke kallon wannan moment din da za ta yi tare da Uwais a wannan dan tsakanin na rayuwarta like eternity moment. Ammi ta kinkimo mata aikin da ba ta taba shiryawa ba (zama da Uwais a muhali guda). Jin dadinta daya tsoron Uwais da ta ke kamar na mala’ikan daukar rai ya ragu sosai daga zuciyar ta. Tana jin kanta ta daidai da daukar kowanne irin challenge daga gare shi, tunda dai ya bi umarnin mahaifiyarsa bai yaudareta ya baro ta a gida a bayan idanun ta ba. A nan filin jirgin Fahimah ta fahimci tafiyar tasu ta gamayya ce shi da abokan aikinsa. Sai dai mutum daya ne Bahaushe, sauran duk kabilu ne. Wasu cikinsu sun taho da matansu, amma Uwais bai yi introducing Fahimah ga kowannen su ba, su dai sun ganshi tare da mace, kuma da ya ke sun san ya yi aure ba dadewa sai ba su ce komai ba. Domin sama yake da su a mukami, matan biyu sun gaisa da ita, Femi da Ronke, amma yadda ta ga Uwais na harararta sai ta kama kanta bayan gaisuwar ba ta kara kallonsu ko shiga sha'anin su ba. Da kananan motoci na GT Bank aka zo aka kwashe su zuwa masaukin da aka tanadar musu a (Cascade- Wellness Resort Hotel). Hotel ne mai kyau sosai a Ikoyi ta jihar Lagos. Ta lifter suka bi zuwa dakin su, Uwais ya sa key din da aka ba su ya bude. Fahimah bata san lokacin da ta yi catching numfashinta dinta da karfi ba, da ta fahimci dakin falle daya ne tal, ma’ana ba ciki da falo bane bedroom ne guda daya. Amma gadon dakin babba ne sosai yadda sai mutum biyar su kwanta ba tare da daya ya gogi daya ba. A gefe ga sofa-bed, sai tebirin aiki da study-lamp daga can gefe. Bedside fridge da tv a jikin bango, sai wardrobe ta kayan sawa, bayan wannan babu wani tarkace a dakin, very neat ga rabar A/C na fita ko ta ina da kamshin room freshner mai sanyi, kuma komai dake dakin daidai bukatar kowanne dan Adam ne. Uwais bai ce wa Fahimah komai ba yana aje trolley dinsa ya yi zaune gefen gado yana latsa wayarsa. Wayar Ammi ya kira don ya ji saukar ta, amma ba ta shiga ba, sai ya aje wayar ya fada toilet. Wanka ya fara yi sai alwallah, ya yi brush sannan ya fito daure da towell iya kugunsa. Har zuwa wannan lokacin Fahimah na nan tsaye inda ya barta tana sakawa tana kwancewa. Ko da ta daga ido ta dubi Uwais daure da towell saura kadan fitsarin da tuntuni ya cika mata mara ya balle ya zubo. The extra-ordinarily well-built structure, the physique chest, the muscles and masculine appearance su suka taru suka kusa nakasta ‘yan kananan idanunta. Fahimah tayi maza ta runtse su gam-gam ba ta kara budewa ba, jikinta na mazari kamar wadda sanyin kankara ke kadawa. Sauri ya yi ya zura jallabiya a jikinshi don shi ya manta ma tana dakin. Da bai fito a haka ba, kada ta raina shi ko ta kalle wa Amrah miji. Gara ya je ya nemi wani dakin ya kai ta, shi ba zai iya kwana da mace a daki ba Amrah ba. Ya tada sallah, a ransa yana fadin, idan kafafunta suka tara jini za ta zauna ne. Bayan ya idar, ya kira kan talfon ya yi odar abincin mutum biyu ba tare da ya tambaye ta wanda ta ke so ba. Ya san dai abincin gidansu kullum ganye ya fi yawa (vegetables) don haka abin da ya yi order kenan, sai white rice and stew da farfesu. Ba jimawa aka kawo, lokacin ta gaji da tsayuwar da runtse idon kamar yadda yayi hasashe ta shiga toilet. A yanayin da ta ke jin jikinta ga gajiya ga takurar period wanka kawai za ta yi ta ji dadi, don haka ta yi wankan, ta kimtsa kanta, ta yi brush sannan ta maida kayan jikinta ta fito. Samunshi ta yi yana cin abinci. Looking smart and gentle a duk abin da yake yi. Uwais, ba zai daina tafiya da ruhinta ba watakila har gaban abada! Komai nasa mai ban kaye ne ga zuciyarta, ba tun yau ba ta dade tana satar kallon sa in yana cin abinci. Wani irin gaye yake komawa mai yanga idan yana cin abinci amma ba wai ya san hakan ba shi. Actually bai san me ya sa ba, jin haushinta da tsanarta da yake sun dan ragu, but bai da wani feeling ko kankani a kanta. Ya sa wa ransa ta zame masa dole, dole kuwa ya yi hakuri da ita ya sawa rana juriya in yana son farin cikin Ammi. Ya yarda wholeheartedly Ammi ke son Fahimah wato da dukkan zuciyar ta, da kyar in son da ta ke matan bai rinjayi wanda ta ke masa ba. Da zamanta shiru ya ishe shi sai ya ce. “Abincin ma jira ki ke in ce miki ga shi ko? Ashe kuwa za ki kwana da yunwa, look, ki rage wadannan mayun idanun naki a kaina kada ki sa in kwareâ€?. Uwais ya fada ganin ta je can karshen dakin ta zauna a dofane tana kallon sa, ba tare da ta bi ta kan abincin ba. “Malama, ki yi maza ki ci mu je in kama miki daki, kada matata ta jiyo tsamin jikin nan naki ta wayaâ€?. Wani murmushi Fahimah ta yi, maimakon maganarsa ta bata haushi, he noticed the murmushin, sai dai bai san ma’anarsa ba. Bakar magana ya gaya mata wadda kowacce mace ka gaya wa ranta zai sosu. Burin sa har kullum shi ne bacin ranta, muzantar ta da wulakantar ta. To ta daina bari wani abu nasa ya bata mata rai don ba zamansa ta ke yi ba. Ba ta ci abincin ba har ta yi shirin kwanciya, a ranta tace ka ci kai kadai ka kara zama katoto dama gaka nan masha Allah. Duk da irin kartawar da cikinta ke yi, ta gwammace ta barwa Uwais abincin sa tunda har ya ce tana tsami. Ta ji haushi don haushi amma ko a fuska bata nuna ba. Uwais kuma bai kara ce mata uffan ba, ya harde bisa gado sai faman kiraye-kirayen waya yake yana zuba turanci kamar bakon Ba’ireshe. Fahimah ta dauki filo daya ta jefa kan sofa ta rufe kafafunta da katon hijabinta ta yi kwanciyar ta. Waya ta karshe da ya amsa ta fahimci da matarsa ne, kuma maganar da yake yi ba cikin dadin rai yake yin ta ba. With a bitter tune take fita fiercely. Duk da haka a tausashe. 9/23/21, 8:19 PM - Buhainat: “Whatever Amrahâ€? whatever makes you to disgrace me ta hanyar tafiya babu izni na. Ga dan iska ko? Wanda bai isa ba, bai isa da matar sa ba don kawai yana son ta, tunda ni baki dauke ni a bakin komai ba ki je ki ji da boko, ni ma in ji da loneliness dina. Ba'a sayen soyayyah da na sayowa kaina wata, sai dai duk abin da ya faru nan gaba kada ki yi kuka da ni. Ki yi da kan ki. Na fada miki na kara, ban iya rayuwa babu mace tare da ni, this is my hidden nature, ina na akan baka na na ki dawo B.U.K in kina son auren mu ya doreâ€?. Da sauri ya kashe wayar da ya tuna akwai mutum a dakin, shaf ya manta da ita, shi mutum ne mai sirri da ba ya son wani ya ji sirrin aurensa ko yaya yake da shi, balle Fahimah. Gyaran murya ya yi don ya tabbatar ta yi barci ko ba ta yi barci ba? Ta ji sirrinsa da Amrah? Abin da bai sani ba ta dade da kaiwa birnin Sin a barcinta tun sanda ya fara maganar. Har tashi ya yi ya wuce ta gaban sofa din ya tabbatar barci ta ke don ga numfashinta na sauka a hankali. He felt relieved. Ai in ta ji Amrah ta gudu ta barshi sai ta yi dariya ta kyakayata, ta gane son da yake mata ya fi nata yawa wanda hakan abun kunya ne a gare shi, kuma a zahiri ya dade da fahimtar hakan. Ba ya so ya yarda ne da gangan, ya fi alakanta hakan da ra’ayin gidansu, ‘yan boko ne na ga ni kashe ni, wadanda za su iya sadaukar da komai don tsira da profession din su. Soyayya is their last priority. Shi kuma ba shi ya sanya wa kansa soyayyar Amrah ba, Allah ne ya sanya masa, idan za ta zama cutuwa a gare shi kamar haka, yana rokon Allah ya rage masa. Ko ya cire masa bakidaya Ya yi nafilfili masu yawa a daren yau kafin ya kwanta. Da asubah yana so ya tada Fahimah sallah yana kwabar kansa shiga sha’aninta. Kulawa ma ai yabawa ce. Ita da kanta ta tashi ta shiga toilet ta yi changing sannan ta koma ta sake kwanciya. Sai wajejen bakwai na safe ta tashi ta ga Uwais ya tsuke cikin Spanish suit bakake wul, wadanda suka maida shi bature zallah, sai tazar kwantacciyar sumarsa yake yi da kumb yana mulketa da Arganavita. Aka kawo karin kumallo ya karasa ya karbo ya rufe dakin, ya zauna yana ci yana tunanin ya aka yi jiya ya manta bai je ya kama wa Fahimah daki ba? Zuciyar sa ta yi gaggawar ba shi amsa da cewa, “Amanar Ammiâ€?. What if wani ya je ya cutar da ita a bakon wuri, me zai ce wa Ammin ta? Don haka ya cire maganar kama mata daki daga ransa sam-sam, zai ta jure hakurin zama da ita. Da ganin bakar fuskarta. Har Allah ya iyakance masa wannan kaddara, ya dauki aurenta matsayin jarabta wadda yake fatan Allah ya ba shi ikon cinyewa, ya sa ya gama da mahaifiyarsa lafiya. Ammin da yake so fiye da yadda yake son kansa. Yadda Uwais ya dauki aurensa da Fahimah matsayin mafi munin jarrabawa a gare shi, ita Fahima ta dauki aurenta da Uwais ne as a luck by chance, ko Uwais ba zai so ta ba aurensa rumfa ne, mafaka ne, kuma waraka daga tsohon ciwo, tsohon mikin da ya dade yana wahal da ita. Don haka ita ko Uwais ba zai so ta ba, she's now contented and satisfied with everything in life. Ammi ta yi wa zuciyar ta gata, gatan da ba za ta gushe tana mata addu’a ba, tare da roka mata gamawa da duniya lafiya har karshen rayuwar ta. Da ya so ta, da kada ya so ta, yanzu duk uwar su daya uban su daya a wurin ta. A ‘yan kananan shekarunta ta yarda love never fadesâ€? wato soyayya bata taba kodewa (son da take wa Uwais na har abada ne) sannan sai ta ga dama ta ke yin kanta. In haka ne kenan ba ta ga laifin Uwais Shagari da ba ya sonta ba, soyayyar ba ta ga damar yin kanta a kansa ba. Tasa soyayyar a kan Amrah ta ke, wanda ko kusa ba yin kansa ba ne. Ita kuma ta kasance mai yawan yi wa dan Adam uzuri a rayuwar ta, kamar yadda Annabi SAW yayi umarni, don haka komai Uwais zai mata uzuri za ta yi masa, uzuri bayan uzuri sau saba'in, uzuri albarkacin Ammi, da uzuri albarkacin soyayyah. Ya ci abincinsa, ya kira Ammi a waya, ya ji yadda ta sauka, sannan ya gaya mata su ma sun sauka lafiya a jihar Lagos. Ammi farin ciki kamar ta yi ya ya! Ta sa wa Uwais albarka a waya ya fi cikin carbi, yafi sau shurin masaki. Bai taba jin farin ciki a muryar Ammi irin na yau ba. He was astonished! Har haka ta ke son sa da Fahimar? Shi kuwa me zai hana shi ya daure ya ci gaba da faranta wa Ammi, in ya so ita Fahimar ta ci gaba da ganin other side din Uwais ita kadai, uwarsa ta yi ta sanya masa albarka irin haka??? "He who has the blessings of a mother....never loss in life". Ammi ta cancanci samun kowanne irin farin-ciki daga gare shi, sabida bata da kowa sai shi, kuma bata da mai rufawa Fahimah asiri bayan shi, kowa zai auri yarinyar ba zai mata rikon da zai gamsar da Ammi ba, idan aka yi la'akari da asalinta, amma idan shine yasan in reality zai rike auren ta koda a ladan noma ce, sannan ko gunduwa - gunduwa zai dinga yi da ita a bayan idon Ammi, a gabanta ya nuna shi mai kyautatawa ne ga Fahimar, albarka zai yi ta sha kwando-kwando irin wannan a wurin Ammi. Murmushi ya yi mai sauti, a lokacin da ya gama wannan tunanin, har yanzu Ammina kan layi, tana ta zuba masa hirar mutanen Sudan, ya ce, “Ammi ta ki cin abinci tunda muka zo, kuma bata magana, ko za ki yi mata magana kada wani abu ya faru a ce laifi na?â€? Ammi ta ce, “Ba ni Fahimarâ€?. Fahimah na jinsu, a ranta ta ce, ta inda ya koma ke nan? Hada ta da Ammi? Ina ruwansa da kin cin abincin ta? Cikin sa ko nata? Ita bata son munafurci. Ta lura abinda ya koya kenan. Tana karbar wayar ta yi sallama. “Kin ki cin abinci Fahimah, a wane dalili?â€? Idanunta suka cicciko da kwallah, ta ya za ta iya cin abinci yana gasa mata bakaken maganganun sa masu kona ruhin ta, yana hantara da kyarar ta yadda yake so? Shi cin abinci ai sai da sukunin zuciya ake yinsa, ita kuma zuciyar ta babu sukuni ko kankani. Something deep down inside her is disturbed, she is emotionally disturbed. A kan me ya kamata ta yi a duniya Uwais ya so ta? Ta laluba ta ko’ina ta rasa, shi ba irin mazan da wani abu ke jan ra’ayinsu ba ne, tsayayyu ne a kan ra’ayin su da akidun su kamar mahaifiyar sa. Amma daga jiya zuwa yau ta yarda Uwais ya ragewa kansa tsanar ta, tunda har ya iya ya kwana daki guda da ita bai yi amai ba, bai yi bacin ran nan nasa ba. Kuma ko sau daya bai kira ta Goddam Black ba tunda suka bar Kano. Ammi ta sake maimaita tambayarta jin Fahimah ta yi shiru. Wannan karon ta sassauta murya, “Fahimah, me ya sa ki ka ki cin abinci? Ko akwai damuwa ne? Is he maltreating you?â€? Da sauri Fahimah ta girgiza kai, “Ba komai Ammi, lafiya muka zo. Na ji ciwo a hannuna ne kafin mu taho yana dan damunaâ€?. Ammi ta ce, "Zan fada masa ya sa miki magani, ko ku je asibiti a duba. Don Allah ki kula da kwalliya Fahimah, na san ki ba damun ki ta yi ba, ki yi ta yin ta akai-akai, ki zama cikin kamshi kodayaushe, sabida da da yanzu ba daya bane zaman wani kike yi yanzu, zaman samar wa mijin ki hutu da nutsuwa daga ni'imar da Allah ya baki, ki sa a ranki ke amarya ce da ke cin lokacin taâ€?. Maganar Ammi ta karshe ta ba ta dariya, sai da ta murmusa, wai amarya! A'ah muna amarya dai, ita da yake ce wa tana tsami ban da abin Ammi ina ruwansa da wata kwalliyar ta? He may not notice ma idan ta yi tunda ba wani kallon ta yake ba. Ammi ta ce, “Ba abin da ban saka miki cikin kayanki ba na kwalliya da kamshi. Dama ce muka samu Fahimah mu yi amfani da ita, don masu iya magana na ce wa, wai sau daya ta ke zuwa a rayuwaâ€?. Fahimah, ta daga lumsassun idanunta tana kallon kyakkyawa Uwais Shagari na ficewa daga dakin, goye da jakar sa ta kwamfuta ba tare da ya kara bi ta kansu ba daga ita har Ammin, kyau kamar shi yayi kansa, tsaf-tsaf da shi gonin sha'awa wanke hannu ka taba inji Hausawa, miji iya burin kowacce diya mace, kai kace balaraben Kuwait ne ko na Abudhabi ba na Sudan ba, don bashi da duhun kalar su (sudanese) shi a wanke yake tas, bai kara bi ta kansu ba ya fice. Har ya fita ya tuna wayarsa ce a hannunta, sai ya dawo da sauri. A hankali yadda Ammi ba zata ji ba yace. “You Goddam Black, ba ni wayata haka!â€?. Ta mika masa wayar da hanzari, bayan ta ce, “Ammi sai mun sake kiraâ€?. Yana karbar wayar ya sa a aljihu, ya juya yana fadin, “Ko ki ci, ko kada ki ci, ba abin da ya dame ni ba ne fa. Kada ki ji ina gayawa Ammi ki dauka ko na damu ne. Hakkin dake kaina kawai na sauke. Kin gan ni nan idan nas kafa na fita yanzu, sai karfe shidda na yamma zan dawo. Ba zaman mace na zo yi ba da aka lika min ke. Sai ki zauna ki ta gadin daki tunda haka Ammi ke so. Na sa a kawo miki lunch karfe biyu, bayan shi in wani ya buga kada ki bude. I’ve my keys with meâ€?. Fahimah ta yi masa shiru, ya sa kai ya fice da sassarfa don he is almost late. Yau ne za su fara seminar din da ta kawo su a babbar shiyyarsu ta GT da ke birnin Ikko. 9/23/21, 8:19 PM - Buhainat: Uwais ji ya yi kamar kwarankwatsa ta fado a kansa, sai ya soma ja da baya idanunsa a kanta, sai kuma ya juya da sassarfa ya dauki wayoyinsa da mukullin kofar ya juya zai fice. Da wani zafin nama Fahimah ta riga shi kai wa bakin kofar ta babbake ta da hannunta. “Babu inda za ka je Ya Uwais…â€? Wata uwar harara ya zabga mata da idanunsa da suka rikide kamar na wanda ya sha Dagga. “Idan ke uwata ce sai ki hana ni fitaâ€?. “I’m not your mother, but a good daughter to her, amma zan iya gaya mata tabbas. Wallahi ka fita sai na gaya mata yanzunnan ka tafi neman mataâ€?. Duk halin da Uwais yake ciki sai da Fahimah ta ba shi dariya, amma ya gintse bai yi ba. “To shin ina ruwanki in ma na je neman mata? Na ga dai ba ke zan debo cutar in shafawa ba matata mai hada jiki da ni zan shafawa…â€?. “Whatever!â€? In ji Fahimah, “Ita ma ‘yar uwata ce a musulunci, zan taya ta kiwon rigimammen mijin taâ€?. Maganarta ta yi wa Uwais dadi har cikin kokon ransa. Bai san sanda ya kama hannayenta biyu ya rike cikin nasa yana murza yatsunta cikin wata irin siga. “Fah-himah, a woman can care for her husband, ko da tana period din, in dai da gaske kina taya Amrah kiwon rigimammen mijinta, to ki taimake ni!â€?. "Ni BLACK?" Tambayar ta subuto daga bakin Fahimah ba tare da ta shirya ba. Sai kawai Uwais ya ja ta jikinsa a hankali ya rungume ta tsam-tsam, kamar bai ji tambayar rainin hankalin data yi masa ba. Hausawa suka ce baki shi ke yanka wuyaâ€? yau ya yarda da wannan. "Ki ba ni dama ta hanyar ba ni 'yan mintuna kalilan cikin mintocinki masu alfarma, I will show youâ€? and I will teach youâ€? the way you can caressed for your troublesome husband even with period..." . Fahimah ta runtse ido tana jin sakonnin da Uwais ke aika mata na ratsa ta, cikin rawar murya tace "sai ka janye kalaman ka Ya Uwais.... sai ranar da ka daina goranta min kalar halitta ta, ina son kaina kamar yadda kake son kan ka, sai ranar da ka furta kana so na nima a matsayin matar ka in ba haka ba....". "....In ba haka ba sai me?" Ya tambaya cikin kankanuwar muryar data rage masa. Daga haka bai ba ta damar kara cewa komai ba, domin gabadaya ya sure ta zuwa gadonsu, gaba daya ya birkice mata har ta fara tantamar anya ba sake mata shi aka yi a garin Ikko ba, da wani mai tsananin kama da shi? Yaya zata zo da mutum kamar fir'auna a kwana daya ya koma mata Musa??? **** WASHEGARI Daga Fahimah har Uwais sun kasa kallon juna after the incidence, the images of yesterday night, the glimse of the occurances, the gentle love making, the caresses of the mid-night, under the dim-light, wasu scenes ne da suka kasa bacewa daga idanu da zuciyar Uwais da Fahimah. Everything happened majestically in a dignified and inspiring way. Kamar yadda Uwais ya fada ne a baya, "an fidda raini tsakaninsa da Fahhimah", kowanne baki ya mutu, fiffika ta kare, babu wanda ke iya kallon kwayar idon dan uwansa. Ko karin kumallo bai tsaya ya yi ba, idan ya tuna abubuwan da ya yi jiya, wai da wata mace ba Amrah ba, watan ma Fahimah din Ammi, wadda suka tashi gida daya ba irin tozarcin da bai mata ba, al'amarin da ko Amrah bata taba samun kamar sa ba, me ya sa ita wannan harkar ba ta san girma ba ne? Me ya sa ba ta san hakuri ba? Fahimah ta gama sanin sirrinsa da Amrah kadai ta sani, ta san abinda Amrah bata sani bama, me ya saura masa na yi mata fiffika? Ai kawai ya gode Allah ya gode wa Ammi Safeeyyah, ya samu mace daya da daya a cikin mata, wadda ta mallaki komai da yake so a diya mace, in ya ce komai yana nufin komai banda kalar fata. Ga mamakin Fahimah yau karfe hudu na yamma ya dawo maimakon shidda. Ba'a tashi seminar din ba ya nemi excuse ya taho. Yana shigowa ya aje jakar computer sa ya fada toilet ya sakar wa kanshi shower mai sanyi karara. Tana zaune bisa sofa ta harde kafafun ta cikin kayatacciyar kwalliya ta lace cotton ya fito daure da towel da kuma wani karami a kansa yana tsane ruwan da ya jika sumarsa. Ya tsaya a kanta yana tambayar ta da sanyin murya, "Kin ci abinci?â€? A cikin muryar akwai wani irin concern da sauyin amo kamar ba ta Uwaisu ba. Kai ta daga masa ba tare da ta dago ta dube shi ba. Ya ce, “Fah-himah, magana nake yiâ€?. Kanta yana durkushe ta ki dubansa kamar yadda yake so, hawaye sun wanke mata fuska. Uwais ya kama hannayenta ya cira ta tsaye, nan ya gane ashe kuka ta ke yi. “Akoke sarkin kuka you easily cry kamar karamar yarinya, yanzu kuma me aka yi miki?â€? Fahimah da za ta iya da ta gaya ma Uwais cewa; tana kuka ne don rashin sanin takamaimai makomar rayuwarta in sun bar Ikko zuwa Kano. Sannan ta kasa gane a ajin da Uwais ya sanya ta. Daga jiya zuwa yau dai al'amuran sa masu ban mamaki ne da suka sa ta kasa gane inda yasa gaba. So ko rashinsa? Ta kasa ganewa. Idan babu so, abubuwan da ya yi a jiya ba su yi kama da na yaudara ba, sannan sun tsaya mata a rai sun hana ta sukuni tun safe, sun barta emotionally tortured. Ga dukkan mamakin ta kamar Uwais na karanto zuciyarta. Domin murmushin da yake ta yi, tamkar yana gaya mata ne cewa, “Ina hango abinda ke karkashin zuciyarkiâ€?. Ya rage tsawo zuwa dai-dai nata, ya soma sumbatar ta softly. "Kin ga abinda ya dawo da ni, ya hana ni zaman seminar, (these luscious lips....)". Bai kara ba ta damar kowanne bahagon tunani ba sai nasa shi kadai; Uwais Shagari Har magriba Uwais da Fahima ana murzar juna kamar ba gobe. Gabadaya wayoyinsa ya kashe su. Yau ko abincin dare ba su ci ba, tsabar idanunsu sun rufe da dokin juna. Duk da haka ya san limit dinsa, kuma ya kiyaye dokar Ubangiji bai tsallake boarder ba, don shi mutum ne mai kiyaye dokokin Ubangiji. Washegari ya kama tahowar su gida Kano. Tun asubah sun hade komai nasu. Karfe tara za su tashi zuwa Kano, in ka gansu kamar wadanda aka yi wa duka duk ba su da kuzari. A kan dalilin da kowannensu bai sani ba. Kamar ba sa son komawa Kano sam, ji suke kamar su dauwama a Ikko cikin wannan yanayin, Ikko ta bar musu tarihi mai wuyar mantawa, zai iya rantsuwa kwanaki biyun nan da ya yi tare da Fahimah, duk da mai gaba daya ba ta afku ba, ya fi jinsu a ransa da gangar jikinsa da ruhin sa fiye da sati biyun farko na amarcin sa da Amrah. ***** KANO Shigowarsu gida ya yi daidai da kecewa da aka yi da ruwan sama kamar da bakin kwarya. Da gudu-gudu suka karasa shigewa ciki, amma duk da haka ruwan ya taba su. Musamman Fahimah da ta tsaya fiddo jakunkuna. Tana shiga daki ta ji wani sururun sanyi na shigarta, tabbacin zazzabi ya shige ta sakamakon dukan ruwan saman. Ta yi maza ta cire jikakkun kayan ta canza ta nemi rigar sanyi (sweater) ta saka mai kauri, ta shige cikin bargon ta mai tsananin laushi ta kudundune, hakoranta na karo da juna. Bayan ruwan ya tsagaita Uwais ya fito falon, ya dauka zai taradda abinci ta shirya, amma sai ya ga wayam. Ya san gajiya ce ta hana ta, don haka ya koma ya dauko mukullin mota ya fita. Chicken Republic ya je ya yo musu takeaway na fried rice da kaza, sannan ya dawo. A kan dining ya ajiye mata inda da ta fito za ta gani. Amma sai ya kasa wucewa dakinsa ba tare da ya duba ta ba ko tana son wani abu. Nan ya hango ta dukunkune can karshen gado, hatta bargon da ta ke ciki karkarwa yake yi. Da sauri ya janye bargon gaba daya, ya dube ta a tsorace. “Are you alright?â€? Murya can kasa ta ce, “Dukan ruwa ya sa min masassaraâ€?. “Za ki iya takawa mu je a yi miki allura?â€? Cikin azabar zazzabi ta ce, “Ba zan iya fita ba, in ka iya dai ka yi min kawaiâ€?. “Ni likita ne da zan miki allura? C’mmon tashi mu je nan clinic na bayan muâ€?. Reluctantly ta ce, “Ni fa ba zan iya takawa baâ€?. “Then I will help you with thatâ€?. Ya ciccibo ta gaba daya daga gadon akan kafadunsa ya yi waje da ita kamar wanda ya dauki dan shekara biyar. Ba zazzabi kadai ke damunta ba har da ciwon mara mai tsanani, ta dai ce zazzabi ne don ba za ta iya fada ba, kada ya fassara ta da wata manufa. Amma da suka zo tebirin likita dole ta runtse kunyar ta fada, likita ya tambaye ta da ma ta saba tana yi ne? Ta ce, “Eh, in za ta yi al’ada tana yi sosai, amma yanzu ba ta san me ya kawo shi ba, don ta gama period din ma tun safe. Tana kallon-kallon tuhumar da Uwais ke mata irin na me ya sa ba ki fada min ba ni? Bayan kin san i'm patiently waiting for this?â€? Dr. ya yi ‘yan rubuce-rubucensa ya ce da Uwais, “You can take care of that aboki, ba sai ta sha magani ba, da ganin ku an ga sabbin aure, your wife needs youâ€?..â€?. Fahimah kamar ta rushe da kuka jin sharrin da likitan matan nan ke mata. Shi kuwa Uwais ban da murmushi ba abin da yake fuskarsa har wani annuri na musamman ta ke yi kamar Doctor Haladu ya yi masa albishir da abin da ya jima yana jira. 9/23/21, 8:19 PM - Buhainat: “Na baro ta a gidaâ€?. Ya dan fiddo ido a kanta cikin tuhuma, “So you want to me to spend my precious kobo on you? A wane dalili? Ko matata dana ke so ban taba saya wa waya ba zan saya miki?â€? Haushi ya kama Fahimah, ta tsani wannan kwatantatan da yake da matar sa Amrah, mai nuna ta fi ta matsayi. Ai ba sai ya fada ba, ta dade da sanin wannan. Ita matar shige ce Amrah matar So. Kuma ita ba ta ce ya saya mata waya ba, balle ayi mata gorin so, tambaya ya yi kawai ta ba shi amsa shi ne ya zama abin cin zarafi? “Bana bukatar ka saya min waya, Yaya Uwais, bana bukatar komai daga hannun ka". Ta fada a matukar gajarce. Kura mata ido Uwais yayi kadan, yana iya jin little anger din dake cikin tune din muryar ta kadan, mai nuna maganar sa ta tunzura ta, duk da bata daga masa murya ba. “In ma kina bukata ba dai ni Uwaisun ba, sai dai wani mai tsananin kama da ni. Bana kyauta sai ga wanda nake so, in kuma za mu yi deal ne, to mu yiâ€?. “Deal?â€? Fahimah ta fada a hankali da sigar tambaya. Cikin alamu na rashin fahimta. Don bata fahimci akan me yake magana ba sam. “Yes! Deal!â€? Uwais ya fada, yana matsowa gabanta cikin takunsa na kasaita majestically, hannayen sa duka biyu zube cikin aljihu. “In ba ki Iphone dina, kiyi ta hira da Ammin ki, kin ga ni har uku gare ni, amma ba'a banza ba, ke kuma ki yi min tausa (become my messeuse) daga yau har mu koma, gabbaina duka ciwo suke, na dade ba ni tare da matata.... She left me stranded (abandoned, helpless) andâ€? Iâ€? want to be caressed (matata ta bar ni a gantale, kuma ina son kulawar maceâ€?)â€?. Ya mika hannu ya kamo kafadun Fahima in a gentle way, kwayar idanun sa mai sheki na nuna bukatuwar miji zuwa ga matar sa (sexual urge). Saura kadan Fahimah ta saki fitsarin da da take ji tun a mota. Idan akwai abin da ya fi shock to Fahimah ta shige shi a daidai wannan lokacin. Ta kasa gane me ke faruwa yau, "Ikko Ikon Allah kawai!" Ta ayyana a ranta. Ko me ke shirin afkuwa da rayuwar ta kuma? Da alama rayuwar ta dauki another giant direction. Uwais is touching her attractively wanda ke nuna he is attracted to her kamar yadda ya fada (he want to be carassed). To tun yaushe wannan sabon al'amarin kuma ya fara ginuwa a zuciyar sa? Wani tunani ne ya zo wa Fahimah.......a lokacin da Uwais ya kawo bakin shi dab da nata, da niyyar kai mata sumbaâ€?... (Wato a rashin uwa za a yi uwar daki da ita) since his loving wife left him strandedâ€? ita ga ta sarkin taimako, kwaryar da babu ta tsada, wadda da an kwankwasa ta za'a samu abinda ake so ko? Shine za'a fake da wani 'deal'. Ita da aka ce ba'a so, ba za'a taba so baâ€?.... dare da rana ana kara maimaita mata kalmar 'rashin son' don ma kada ta manta ta yaudari kanta, ita da aka ce mummuna ce, "Blacky" ko sunanta ba a iya fada, sabida bata kai matsayin mutum a idanun sa ba, amma wai jikinta ne za'a yi maneji da shi yauâ€?.??? How dare Uwais wants her to believe these nonsense? Da mugun sauri ta ja baya…tamkar ya dala mata wuta. Bayan ta doke hannayen sa daga kafadun ta. Uwais ya dan dube ta da mamaki, kwayan idanunsa sun kada har sun shige ciki. Tabbacin abinda yake fita bakin sa daga gangar jikin sa ne. Takawa ya yi a hankali ya sake binta, ta cira kafa za ta ranta da gudu, Uwais ya cafko hannayenta ta baya. Kallonta yake da reddish eyes dinsa cikin wata irin murya ya ce, “Are you fighting me? You better stay calm, in ba haka ba wahala za ki sha a hannu na, bani da compassion ko kankani a wannan fannin sai akasin sa. Ai na ce is a 'DEAL' so don’t worry I will pay for itâ€?. Don haushi Fahimah ji ta yi kamar ta wanka masa mari, ta sake wanka masa ko ya bude munafukan idanun sosai daga lumshe sun da yake faman yi, ya gane da wadda yake tare, don da alama ya makance, da karfi ta ce, “Sunana FAHIMAHâ€? I’m not AMRAH! Kuma ni ba karuwa bace da za'a biya a taba jikin taâ€? Wata fizga Uwais ya yi mata zuwa sofa-bed, ya ce, “I knowâ€?..... i know u 're not Amrah.....ai taimako na ce ko? Itama Ammi ta turo ki don ki taimaka min ne. Kuma ba a kyauta ba, i will pay for everything.....â€?. Daga haka ya kai bakinsa saman nata ya soma wani irin kissing din ta tun daga kolouwar ran sa ba tareda ya sani ba. Duk kokarin Fahimah ta kasa kwatar kanta a hannun Uwais, ya birkice mata gabadaya hungrily yake kissing din nata, it was like he is enjoying kokawar da suke yin, don sosai ya bada himma ga taya ta kokawar ko a jikin sa. Bakin ya samu a dai-dai yake ta sumbata yadda ransa yake so tamkar zai raba ta da luscious lips din nata. Da alama tun jiya yake kintata how soft and sweet it will be. Fahima ba ta san ma’anar abin da ya ce ba, lokacin da yake mata magana cikin lallashi, amma ta fahimci ko ma mene ne ba cikin hankalinsa yake fada ba da ko kusa ba zai soma ba. Ba'a dauki wani dogon lokaci ba, ita kanta ta soma fita daga saiti balle shi da yake a kan network tun jiya dauriya kawai ya dinga yi don tsira da pride dinsa. Har zuwa yau da ya fahimci pride din babu inda za kai shi gara kawai a fidda raini tsakanin shi da Fahimah, ta san cewa ba sai da so miji yake taba matarsa ba. Wannan al'amarin daban yake. It's a call of nature. A kuma duk lokacin da tayi kira bata san dai-dai da ba dai-dai ba. Ba kuma kowa ya janyo masa wannan rainin da zubar da kan ba yau sai Amrah. Da ta yi zamanta dakin aurenta wata mace ma ta isa ta ganshi balle har ya nemi hakkinsa azo ana kokawa da shi kamar dan dambe? Matarsa caressing dinsa ta ke with so much affection kamar jariri, ba ta taba nuna gazawa ko gundura da bukatunsa ba. Fahimah, ta ga cewa kokawarta, protest dinta da dan karfin da ya rage mata bai isa ya kwace ta hannun Uwais ba, idan kuma ta kyale shi za su aikata haramci domin jini bai dauke mata ba, amma da wane language za ta yi wa wannan mayunwacin Zakin magana ya saurare ta har ya gane abin da ta ke fadi? Da za ta iya cutar da Uwais cizonsa za ta yi, amma ina! Ko mintsininshi ba ta iyawa, kuma idan ta ce itama ba ta enjoying wadannan deep kisses na Uwais Shagari ta yi karya, ta kwana da yunwa. Dama ce ba ta so ya samu a kanta, dama irin wannan data kunshi dukan pride dinta na diya mace, tunda ba son ta yake ba; he just want to take advantage of her body and left her stranded shima kamar yadda matar sa ta Soyayya ta yi masa. Tunanin hakan ne ya sa wani karfin zuciya ya zo wa Fahimah. Ta janye da karfi daga Uwais, sannan ta saki kuka mai tsuma rai. Ta durkushe a kan kafafunta fuskarta a tsakanin cinyoyinta. Kuka ta ke mai ratsa zuciya na tausayin kanta. Da tunanin duka wadannan sensual touches da Uwais ke mata ba ya sonta ko da kankani, yana yi ne domin ya taimaka wa kansa, su koma Kano ta ci gaba da zama a dakin mahaifiyar sa ya koma wajen matar da yake so su cigaba da rayuwar su ya manta da ita. Sai ganin Uwais ta yi ya biyo ta ya durkusa, ya dora hannunsa bisa gwiwoyinta. Idanunsa kadai sun gaya mata ba asalin Uwais ba ne da ta sani, he’s in urge don haka ba Uwaisu ba ne sarkin izza, ba irin dadin bakin da bazata ji ba yanzu don ya samu abinda yake nema a wannan takaitaccen lokacin. “Ki fahimce ni Fah-himah... (daga ji ko iya fadar sunan bai yi ba, yau ya fara koyon fade). Ina da damar in nemi hakan daga gare ki sabida yadda na biya sadakin Amrah, babu bambamci da yadda na biya naki, I didn’t say I love you balle kice karya nake ko na canza (doctrine) dina a kanki, just ki taimaka min yadda Allah ya taimake ki, komai ki ke so zan miki. I’m your husband even without love, abinda zaki duba kenan, wani irin mutum ne ni Fahimah mai wannan weakness din, bana iya zama haka tsawon lokaci, zan halaka. Idan Amrah ta guji ladanta da aljannarta ke ki karba Fah-hima, na yi miki alkawarin daga miki kafa ki shige aljannah unquestionably. I promised it will not be hurting, just loving and romantic, Fah-himah, idan kin duba rashin kyautawa ta a gareki kin yi la'akari da ita kin hana ni, zan fita a daren nan zuwa inda zan biya kudi na a ba ni. Kada ki manta a Lagos muke ba a Kano ba, kasa kawai zan sauka suna nan birjik suna jira a reception da bakin beaches. Ke da Amrahn in ya so duk kun zama ‘yan wuta, don wallahi dukkanku na yi zina ba zan taba yafe muku ba…â€?. Wani irin tsoro mai tsanani ya kara kama Fahimah. Ta daga kumburarrun idanunta tana kallonsa. Yana kara jaddada mata ba ya sonta, amma yana rokon ta ba shi jikintaâ€? Uwais wane irin mutum ne selfish haka, ko me ya dauke ta? Dabba ko mara hankali? Har da wani cewa kome take so zai yi mata, ita almajira ce? Ina ruwan ta da abin hannun sa? Ko dai Yaya Uwais yana dan taba shaye-shaye ne? “Ki yi min kallon wanda ya sha kwaya ko Dagga (marijuana) daidai ne, in dai za ki bar ni Fahhimaâ€? yau kawai, sau daya., just once…â€?. Fahimah ta kara ja da baya, as he is coming closer and closer...â€? “Bana nufin in sa miki karfi, ki bi ni a hankali tunda na lallashe ki, na durkusa miki, abinda ban taba yiwa ko matata ba, the last attempt will be otherwise…â€?. Fahimah ta daga jikakkun idanunta tana kallonsa jin abin da ya ce. A sanyaye ta ce, “Will you rape me idan na ki?â€? A hankali ya daga mata kai tare da lumshe rinannun idanunsa in affirmation, wato cikin tabbbatar mata da zai yi hakan. Babu shakka. Sai ta ce cikin karkarwar murya. “Ko da ina period ne? I mean jinin al’ada?â€? 9/23/21, 8:19 PM - Buhainat: Idanun Fahimah suka rufe ruf! Sabida bakin-ciki. Ita ce akwalar kenan? Za ta shayar da Uwais mamaki, ya karawa kansa bakin fenti a idanun ta, za ta nuna masa kowacce mace sunanta mace, kuma ta fi karfin a yi maneji da ita don tana marainiya mara asali, kuma zabin mahaifiyar sa. Dakin ciki da falo ne, don haka falo ta koma ta haye bisa doguwar kujera ta rufe jikinta da mayafin ta, ta yi addu’a ba ta san sanda barci ya dauke ta ba sabida gajiyar da ke tare da ita. Duk yadda ya yi don ya samu barci a daren nan Uwais ya kasa. Jan ajinsa da izzarsa da jin kansa na rokonsa kada ya kara attempting neman wani abu daga Fahimah tun daga sanda ta yi rantsuwa kan cewa ba za ta ba shi budurcinta ba alhalin ta san ba ya sonta. Sai ya hau lalubawa sako-sako wai ya nemo rashin son nata daga zuciyarsa a daidai wannan tsakanin, inda ya fahimci ya yi decreasing gradually da 50% a lokutan da suka kasance tare a Ikko. Amma ya fi karfin ya yi fyade ga matarsa, ko da hakan na nufin ya koma yin azumin tadauwa’i kullum. To amma a yau akwai babbar matsala tare da shi da Fahimah bazata gane ba, da ta tausaya masa koda itama bata son nashi, da ta yi don ceto da neman aljannah, azumi kuma sai gobe zai iya daukar sa. Cikin dare Fahimah ta ji sanyi na kada ta, sanyin da ba ta san daga inda yake ba. Tashi ta yi ta kashe A.C amma ko da ta koma ta kwanta sai ta ji hakoranta na haduwa da junansu. Cikin abin da bai wuce minti goma ba wani irin zazzafan zazzabi ya rufe ta. Ga mayafin da ta rufa da shi ji ta yi kamar babu shi, ta rasa inda za ta sa kanta da sanyin da ta ke ji, sai kakkarwa ta ke. Ta ga cewa in ta yi shiru ta kuma kwana a haka, to da safe kam gawarta za a kai wa Ammi. Bargo ta ke so ko ta halin kaka don haka ta mike da dafa bango ta shiga dakin da ta baro Uwais da zummar dauko bargo ta dawo. Ashe da rabon za ta yi mummunan gani, ganin abun da ya narkar da duk wata soyayyar Uwais daga zuciyarta. Duk wasu emotionsâ€? duk wasu dadaddun mikin soyayya na shekara da shekaru suka ware, suka kama gabansu. Fahimah ta ambaci innalillahi wa’inna ilaihi raji’un, sannan ta sakar masa kofar da gudu ta juya zuwa falon da ta fito. Uwais ya razana, ya kuma ji kunya irin wadda bai taba ji a rayuwarsa ba. A zatonsa ta jima da yin barci, kuma ko ma me ya yi daga ita har Amrah sune masu babban kamasho. Gara ita Amrah a bisa yarjejeniyar da ya aure ta kenan, daga baya ne ya ga ba zai iya ba, ita kuma ta yi kan gaban kanta, amma ita fa? Ita Fahimar fa? Hujjarta ta fi ta Amrah rauni, hujjarta shi ne ba ya sonta, don haka ba za ta ba shi kanta ba, to ko yana sonta ko ba ya sonta yana da wannan hakkin a kanta. Allah ya bashi. Amma ta yi rantsuwa sai ranar da ya furta mata kalmar soâ€? an gaya mata son kirkirarsa ake yi, ko ana karyarsa??? Bai jin sonta, amma a halin yanzu bai jin kiyayyar ta, ya fara sabawa da ita, sannan yanzu abin da ta gani ya sa ya ji nan duniya babu wanda yake jin nauyi da kunya kamarta. Wane tsautsayi ya kai shi? Abu ne da bai taba yi ba ko a lokacin samartaka, sai yanzu da ya mallaki matan sunnah har guda biyu? Ya mike yana maida jallabiyar jikinsa, har ya sauko daga gadon da niyyar binta, wata zuciyar ta dakatar da shi. Yanzu ko me zai ce mata zai zamo ihu ne bayan hari, ko ko ta ce borin kunya ne. Wanda a zahiri haka ne. Ka kasa jin kunyar Ubangijinka sai kunyar Fahimah? Komawa ya yi bakin gado ya zauna ya dafe goshinsa da hannun damansa yana fadin, “Astagfirullah Ya Allah! Wa'atubu ilaikâ€? Fahima saboda kidima bandaki ta shige ta kulle kanta. Tuni ta nemi zazzabin da ta ke ji ta rasa, ji ta yi ta tsani Uwais ba ta ko son sake ganinsa. Ba ta san ma’anar abin da idonta ya gani ba, amma jikinta ya ba ta ba abu ne mai kyau ba, abu ne na haramci ko daga yadda Uwais ya yi da ya ganta duk da cikin dim-light ne. Kuka ta saki mai sauti, ta kwantar da kai a jikin sink tana ta yi. Kukan da ya je har kunnen Uwais, ya rasa inda zai sa kansa, ba damuwar Fahimah ce damuwarsa ba, a’ah, mutuncinsa da girman sa a idanunta. A haka suka wayi gari, hasken asuba ya ratso ta tagar toilet din, tana rangaji ta yi alwallah ta fito ta yi sallah, tana idarwa ta yi lullubinta sannan ta shiga inda Uwais yake. Yana kwance saman gado, ya dafe goshinsa da hannun damansa. Nadama goma da ishirin ta damesa. Kafafunsa zube a kasa. Ya yi nadamar abin da ya yi din a daren jiya, kuma tun jiya yake istighfari, a fili da boye, zuciyar sa na mai sakancewa da cewa Ubangiji ya amshi tubansa, tunda shi Yace "ku tuba da niyyar bazaku sake komawa izuwa zunubi ba". Kallon da Fahimah za ta ke masa shi ne babbar damuwarsa. Dauka zata yi tuntuni rayuwar sa kenan. Daga bakin kofa ta tsaya, muryarta ta dushe don kuka har ba ta fita sosai, ta ce. “Ka zo ka maida ni wurin su Ammiâ€?. Ya daga rinannun idanunsa ya dube ta, ta kauda kai. Jin wani abu kamar kibiya ya fito daga idonsa ya shiga nata. Uwais ya taso daga kwanciyar gaba-gadi ya tako ya tsaya a gabanta har tana iya jin hucin sassanyar numfashinsa. “Da ni na kawo ki? Ko ni nace ki biyo ni? Ban ce ki bi Mahdi ku koma ba kika ki? Ban gaya miki zuwanki baya amfana min komai ba? Ya tambaya a jere, da wata murya tamkar zai doke ta. Sannan ya sa hannu ya dago habarta. “You can tell the whole world kin gan ni ina abin da ki ka ga ina yi, amma in mahaifiyata ta ji, na rantse sai na sauya miki kamanni, yadda in na sake ki ba wanda zai yarda ya kwashe ki, don ba za ki ganu ba wallahi Fahhimahâ€?. Fahimah ba ta san sanda ta buge hannun Uwais daga habarta ba, duk wani shayinsa da ta ke ji ada, ai yanzu babu shi, ya gama bata rawarsa da tsalle a idanunta, ta ce, “To ka sakenin mana, sai me in ka sake ni? Sai aka ce bazan rayu ba ko a gidan mu na marayu ne? Menene a auren naka banda bakin-ciki? An gaya maka ko ba ka sake ni ba akwai sauran zama a tsakanin mu? Allah ya tsare ni, wallahi ko Ammi za ta min baki yaya Uwais na gama auren ka. I never know this is your habit, Amrahn ma na tabbata bata sani ba wallahi da bazata aure ka baâ€?. Ta saki kukan da ya taho tun daga kololuwar zuciyar ta. Ita kuma kalolin kaddararta ke nan? Daga wannan sai waccan? Uwais da ta bai wa dukkan so da kauna ashe haka yake? Sabon Allah kiri-kiri da aurensa da komai? So ta ke ta gane ko matsayinsa da soyayyarsa sun ragu a zuciyarta a dalilin hakan? Ba raguwa kadai ba, komai ya zagwanye hatta shakkarsa da ta ke ji ta kau (istimna'i yana daukewa mai yin sa kwarjini, yana sabbaba illoli ga lafiya da yawa sannan haramun ne a addinance). Uwais ya yarfa hannuwa ya ce, “Well, ki gaya ma Ammi ga abin da ki ka ga ina yi, ni ma in gaya mata cewa kin yi rantsuwa da ki hada jiki da ni gara kin mutu. Ni ma na mutu kowa ya huta.... A dalilin ba ni da mafita ne kuma na fita a tunanina, na nema wa kaina relief, amma ko ki yarda ko kada ki yarda ban taba yi ba sai jiyan, kuma inda wanda ya sanya ni a wannan halin to ba wata ba ce, ke ce Fahhimah…â€?. Yana gama fadin hakan ya yi dialling number din Mahdi. Mahdi ya ga kira da sassafiyar Allah, sai ya dauka ba lafiya ba. Yana dagawa ya ce, “Please Mahdi come and take me to airport, and take this girl to Ammi, ka gaya mata zan kira ta a waya, wani muhimmin uzuri ya taso min a ofisâ€?. Mahdi ya amsa da, “To ga shi nanâ€?. Har zuwa wannan lokacin Fahimah na tsaye a inda Uwais ya barta kamar mutum-mutuma, tana mai tauna kalaman Uwais a bisa ma’auni na hankali da tunaninta. Ba'a fi minti goma ba da kiran wayar Mahdi ya kira shi, cewa yana reception sannan ya gaya wa Ammi batun tafiyarsa ta ce, lallai ya biya da su wajenta kafin ya tafi. Cikin takaici Uwais yake dubansa, “Me ya sa ka yi min wannan karambanin Mahdi?â€? Mahdi ya ce, “Ta ya ya ba zan yi ba? Ka zo da niyyar yin kwana uku, washegari ka ce za ka tafi, don kawai matarka ta bata maka rai, sai in kyale ka ka bar kasar ba tare da sanin Ammi ba? Don ta ce da hadin bakina ko?â€? Tsaki ya yi cikin haushin Mahdi, sannan ya wuce gaba, Fahima ba ta yi wata-wata ba, ta rufa masa baya harda gudu-gudunta. Fatanta kawai ta bude ido ta ganta gaban Ammi ba tare da Yaya Uwais ba. Ta tsane shi yanzu kam ba ta ko son ganinsa. Allah wadaran soyayyar. Ammi ta tsura musu ido suna sunkuye a gabanta, kowanne fuska ba walwala, da alama Fahimah kuka ta ci ta koshi. Sai ta ji duk farin cikin da ta ke ciki ya koma. Ta dubi Uwais da idanun rahma, ta ce. “Me ya faru za ka tafi unexpected kuma ba tare da Fahimah ba, ka san ba zai yiwu ta yi har sati biyu a nan ba saboda makaranta, kuma na yi zaton kwana uku aka ba ka?â€? Uwais ya ce, “Ammi ba abin da ya faru, aiki ne kawai ya taso minâ€?. Ta dubi Fahima, “Ke ma ba za ki gaya min ba? Kukan me ki ke yi? In laifi ya yi miki ki gaya min kin san ba zan kyale shi baâ€?. Da kyar Fahimah ta motsa bakinta, ta ce, “Ba abin da ya yi min Ammiâ€?. Tana kallon yadda Uwais ya saki wata boyayyar ajiyar zuciya. Haushi ya kama Ammi, ta ce, “To tunda haka ne, ku yi ta rikon bacin ranku a ranku, amma ba inda za ku je sai kun yi kwanakin da ku ka zo da niyyar yi, kun zaga dangi kowa ya ganku. Uwais ina gaya maka ina kara gaya maka Fahimah amanar Allah ce a hannunmu in ka cutar da ita Allah ba zai barka ba…â€?. Uwais bai san sanda ya katse ta ba, “In kuma ita ta ke cutar da ni fa? Ita sai Allah ya barta? Ammi na yi kokari na tausa zuciyata na karbi amanarki ko da bana jin sonta a raina, amma ita tana neman halakar da ni, don haka Ammi ki daina jin tausayin Fah-himah don kuwa ba abun tausayi ba ce, muguwa ce…â€?. 9/23/21, 8:19 PM - Buhainat: Ammi ta kusa yin dariya don tuni ta je gano ga matsalar tasu. Ta dade da sanin wannan cewa; Uwais irin mahaifinsa ne, in haka ne kuwa ba za ta sha wahalar sanya Fahimah a zuciyarsa ba, wuyarta mu'amalar aure ya gitta a tsakaninsu. Ammi ta gyara zama tana murmushi, ta ce, “In dai ka hakura da tafiyar a yau, to ka je ku ci gaba da karbar gaisuwa. Ni kuma zan yi magana da Fahimahâ€?. Ya tashi ya fice ba tare da ya ce komai ba, sai ma kafar Fahimah da ya kusa takewa, Ammi ta bi shi da kallo tana ajiyar zuciya. Uwais na bada baya, Ammi ta ce. “Yo ke Fahimah, an gaya miki ana hana miji wannan ne a zauna lafiya? It's the greatest weakness of men, sannan hanya mafi sauki ta shigewa sukuf zuciyarsu. Ni dai a matsayin uwa nake miki magana ba suruka ba. Don ni ke na haifa ba Uwais baâ€?. Idanun Fahimah suka cicciko da hawaye, amma ga mamakinta ji ta yi ko za a dora mata wuka a makoshi ba za ta iya fada wa Ammi ko wani daban abin da ta kama Uwais yana yi ba, which means har yanzu da dan sauran burbushin son, no matter laifukansa a rayuwa. Kuma ai yace ya tuba, bai taba yi ba, na jiyan ma itace sila. Ita ta ja, tunda ta hana shi abinda Allah ya halatta a gare shi. Ba kuma kowanne dan adam ne mai iya tsallake hudubar shaidan a irin wadannan lokutan ba. Maimakon tace komai, sai ta saki kukan da ke cin ranta. Ta kifa kai a cinyoyin Ammi. Ammi ta janyo ta jikinta ta rungume ta. “Ammi he keeps on telling me cewa ba ya sona, ta ya ya zan iya sakin jiki da shi? Kalmar tana kona min rai Ammi yadda ba kya zatoâ€?. Ammi na shafa bayanta cikin lallashi, ta ce, “Let him say it... let him say it loudly to the whole world ba ke kadai ba, sai ya gama fada zai kore zafin kiyayyar daga zuciyar sa. Kada ki damu da wannan, tunda har mun samu cewa yana son physical relationship (gamayyar jiki) ya shiga tsakanin ku. Wannan ma ba ya zuwa sai da so Fahimah, ki kyale shi ya yi ta fada, watarana da kansa zai janyeta da gwiwoyi a kasa, ko mumbari zai hau yana fadi ba ya son naki ya je ya yi, amma ki barshi ya dabbaqa sunnarsa, sauran ki bar wa Allah ki kuma zuba ido ki sha kallo. Allah fa na sonki da Uwais, shi ya sa ya kautar da hankalin matarsa daga kansa ta nisance shi,da tana nan bazamu taba samun kansa haka ba, don haka Fahimah yanzu lokacinki ne kada ki yi wasa da damarki don sau daya ta ke zuwa a rayuwa kin ji ko?â€? Fahimah ta gyada kai. Ammi ta ce, “To tashi mu je mu karya kumallo, na tabbata ba ku ci komai ba ku ka fito. Shi ma zan sa a kai masa nasa yanzuâ€?. Ba su kara haduwa da Uwais ba sai da daddare, ya shigo a gajiye ya yi wa Ammi sallama cewa zai wuce masauki. Ko da abin da ta ke so? Ammi ta yi murmushi ta ce, “Tunda ka fasa tafiyar ka ji maganata na gode Uwais, Fahimah tashi ku je, Allah ya ba mu alkhairiâ€?. Fahimah ta yi kicin-kicin da fuska daidai lokacin da Uwais ya dago suka hada ido, harara ya sakar mata, ba ta bata lokaci ba ta rama, sannan ta mike don Ammi ta sake maimaita umarninta. Suna tafe a hanya Mahdi ke tuki ba wanda ya kula dan uwansa, sai wakokin (Sudanese singers) da ke tashi a cikin motar cikin harshen larabci ta shahararren mawaki Mahmoud Abdul’Aziz. Suna isowa Fundaq Mahdi ya ajiye su ya juya, Uwais sai da ya tsaya a reception ya karbi mukullin sannan suka haura ta lifter zuwa dakinsu. Tunda suka shiga dakin bai kula Fahimah ba, ita ma ta kama kanta ba ta shiga sha’aninsa ba, amma ta ki barin dakin da yake a kan dalilin da bata sani ba. Mafi rinjaye na zuciyarta ya fi raja’a a kan ba za ta kara nesanta kanta da shi ba, ko da kuwa ba za su hada shimfida ba. "Yaa Allah! May not evil did come again to my husband". (Addu'ar Fahimah a zuci ga Uwais). Filo ta dauka ta jefa bisa kafet ta kwanta. Uwais yayi duk abin da ya saba yi kafin ya kwanta, sannan ya yi changing zuwa Pajamas ruwan toka, ya yi niyyar kiran Amrah kuma sai ya fasa don har zuwa yanzu ba su shirya can-can ba, ita ke nacin kiransa tana ba shi hakuri yana gasa mata bakaken maganganu ta cikin ruwan sanyi, kuma dai bai son yana kiranta gaban Fahimah a kan dalilin da bai sani ba. Amma sai ga nata kiran ya shigo. Da farko kamar ba zai dauka ba, don ya gama shirin kwanciya, ko me ya tuna sai kuma ya dauka. “Habib-Qalby I’m missing you terriblyâ€?. Ya kyabe baki, ya ce, “Amrah how dare you want me to believe this?â€? Ta ce, “Ka yarda da ni Allah kewar ka nake yi ba 'yar kadan ba. Yanzu haka ga ni nan a cikin jirgi na taho in yi surprising din ka, zuwa asubah zan sauka a Kano, I will stay with you for two weeksâ€?..â€?. Idanunsa suka firfito waje, yana duban center din da Fahimah ta ke, ya ce, “Stop joking Amrahâ€?!â€?. “Believe me, I’m not kidding Habiby, amma Daddy bai san na taho ba. Don Allah ko Yaya jabeer kada ka gaya wa na zoâ€?. Har ransa ya ji dadi, don ta nuna ta yi nadamar abinda tayi masa, amma sai ya ce, “Amrah currently bana Nigeria, ina kasarmu Sudan, Yayan Ammi ya rasu. Amma in kin sauka ki jira ni nan da kwana uku zan isoâ€?. Amrah ta ce, “Kai ma ka san tsoro na bai bari na in iya zama a gidan ni kadai. Allah Ya masa rahmaâ€?. “Hakuri za ki yi Amrah, I’ll make sure na dawo in two days. You know how much I missed you babyâ€?. Wani mikakken tsaki Fahimah ta saki, wanda ya sa Uwais saurin toshe wayarsa, gaba daya ma sai ya kashe wayar cike da fargabar ko Amrah ta ji? Tashi ya yi ya kunna wutar dakina fusace, dakin ya gauraye da haske. “Wa ki ke ma tsaki?â€? Daga kwancen da ta ke ta murguda baki, ta ce, “Da wanda ya tsargu da shi nakeâ€?. Uwais ya sanya hannu ya dauke mayafin da ta rufa da shi, ya ce, “Fahimah ki ke ko Fahummah? You better be careful da ni don a fuska ne nake da kyau, idan ki ka shiga hannuna za ki san na fi ki rashin tausayi. It’s my old principle that I will never rape my wife amma da tuni na goge rainin da na lura ya samu matsugunni tsakanin muâ€?. Fahimah ta mike zaune ta dubi Uwais cikin ido da hasken lantarkin da ya haska kyakkyawar fuskarsa, ta zama tamkar an kara masa hasken fata, ta ce, “Raini na nawa kuma Yaya Uwais? Ni da na ganka kanaâ€?..â€?. Ai ba ta karasa ba ta ji ta kane-kane a jikin Uwais, jikinsa rawa yake sosai with utmost regret to the fullest, a lokacin da yake magana harda taruwar hawaye cikin fararen kwayar idanun sa, “Believe me Fah-himah ban taba yi ba, you caused it all, and I repented to Almighty Allah, jiki na kuma na bani ya yafe mini. Shi mai afuwa ne mai jin kan bayin Sa. Ya kike so inyi? So ki ke in halaka? A kan me ki ke so in gaya miki kalmar da ban shirya fada ba? A lokacin da ban shirya mata ba? Ki ba ni lokaci mana? Ki yarda ba abin da lokaci ba ya canzawa a rayuwar dan adam, kamar yadda Ammi ta ce. Fahimah I hate you before, ba don kalar fata ko zubin halitta ba; bana son kowa ya rabi Ammina, infact kishi ne da ni mai tsanani tun ina yaro, so nake Ammi ta zauna da ni ni kadai, tayi ta so na nikadai, amma ba don abin da ki ke tunani ba. A dan zamanmu tare a Lagos, sai na samu al’amura da yawa suka sauya min a kanki Fah-himah. Ganewa da na yi cewa ke din; you’re extraordinarily different da sauran mata, with exceptional qualities ababen so ga duk namijin da ya san ciwon kansaâ€? Ina kara rokon ki bani lokaci, kada ki tursasa ni wajen furta abin da ba ni da iko a kansaâ€?. Fahimah ta kwanta shiruu! A jikin Yaya Uwais, tana jin wani irin dadi mara misaltuwa a zuciyarta da ba ta taba jin kwatankwacinsa a rayuwarta ba. Kalaman sa sun gama ratsa ta. Ta kasa cewa komai, ta kuma kasa ko da kwakkwaran motsi sabida yadda kalaman Uwais da zurfin muryarshi ke ratsa ta. Uwais ya yi amfani da wannan damarâ€? It was kind of gentle romance wanda ya gigita duniyar Fahimah Shagari, ta kara dulmiyewa a kaunar Uwais yau, har fiye da tarin shekarun da ta kwashe cikin koshin wahala..... And it started from thereâ€? tafiâ€? tafi har tsayuwa ta gagare su. Abu na karshe da Fahimah ta fahimta shi ne, daukarta da Uwais ya yi kacokam a hannun sa. Sauran al’amuran da suka biyo baya masu tsauri da girma ne da suka shallake tunanin suâ€? A lokacin da Uwais ya maida Fahimah a layin sauran mata, kuka ta saki mai sauti tana kiran sunan Ammi, kai har Baba Talatu yau ta sha kira, tunda su kadai ta ke da su a duniya. **** Lokacin da Uwais ya samu nutsuwar da yake matukar son samu kwana da kwanaki, wata da watanni, bai juya mata baya ba, rungume Fahimah ya yi a tsakiyar kirjinsa, yana tambayar kansa was all these not LOVE? Idan ba shi ba ne, mene ne? To ko ma dai ya ya ne ko so ne ko ba so ba ne, shi da Fahimah yau sun zama daya. Duk wani kurarinsa da challenges dinsa a kan Fahimah ya neme su ya rasa, irin matan nan ne da ake kira one in million da sai namiji mai matukar sa’a a rayuwa ke sa'ar mallakar su. (Never judge a woman by her skin colour). Inji Uwais Shagari. Uwais yake fadawa kansa. Ya ke kuma fadawa sauran maza 'yan uwansa, masu ra'ayi da akida irin tasa. Har aka yi kiran assalatu Uwais tunanin da yake kenan, yana rungume da Fahimah, yayin da Fahimah ta yi kukanta ta gaji, barci ya dauke ta. Wani irin barci na kwanciyar hankali. Soyayyar shekara da shekaru da ta ke yi wa Uwais yau ta sarrafa kanta ta bada cikakkiyar ma’ana, ma’anar da daga ita har Uwais, babu wanda ya tsammaci girmanta ya kai hakan....fadinta ya kai hakan.... Tasirinta zai kai hakan... haka karfinta da zurfinta ya kai har haka....!!! ***** WASHEGARI Har karfe goma sun kasa fitowa zuwa gidan gaisuwa, duk da Mahdi ya zo daukarsu sai komawa ya yi, don Uwais ya ce da shi Fahimah ba ta jin dadi ya je ya dawo wajen azahar lokacin ta ji sauki don ta sha magani yanzu ta kwanta. Da gaske barcin ta ke tun wayewar gari bayan ya taimaka mata ta yi wanka, ta yi sallah ta sha tea. Shi kuma ya koma kan study table daga shi sai singlet da wando three quarter ya kunna loptop dinsa ya soma rage ayyukansa na ofis. Daidai lokacin da kiran Amrah ya shigo, sai da ya saci kallon Fahimah ya tabbatar barci ta ke sadidan sannan ya amsa. “Habiby na sauka a Kano, luckly Yaya Jabeer ba ya gari, don haka ina wajen Aunty Murja, in ka iso sai ka zo ka dauke niâ€?. Ga mamakin Uwais Shagari, duk dokinsa na son ganin Amrah da son kasancewa da ita ya yi decreasing 50% fiye da tsammaninsa. Daren jiya ya samu wata irin gamsuwa a auratayya da bai taba samu ba. Ya kuma gane kyawun fuska ko kalar fata ba shi ne mace ba, matan alfarma daban suke. Daban Ubangiji ke halittar su kawai, don ya baiwa namiji mai tsananin sa'a irin sa. Shi ya san he's among the luckiest cikin mutanen duniya daga kwanaki bakwai a baya zuwa yau. “Alright Amrah, see you soonâ€?. Abin da ya ce da ita ke nan, sannan ba tare da ya kara cewa komai ba ya kashe wayarsa. Amrah ta yi sakatoto da waya a hannu, lokacin da Aunty Murja ta iso wajen ta sameta, ta mika mata kofin da ke hannunta mai dauke da tatacciyar madarar shanu mai sanyi (fresh milk). Murjanatu ta ce, “Lafiya dai Amrah?â€? Amrah ta yi rau-rau da ido, idanunta cike da hawaye ta dubi Murjanatu, ta ce, “Aunty Murjaj, ni Uwais ya kashe ma waya, alhalin na gaya masa na yo tattaki musamman tun daga Malaysia har Kano don kawai na faranta masa? Na tsallako karatuna cikin hadari mai yawa? Ba don za ki karyata ni ba, wallahi sai in ce miki jiya da daddare..... da muna waya na ji tsakin MACE tsuwww..... cikin kunnena, ya yi sauri ya kashe wayar ba tare da mun yi sallama ba. Yau kuma very shortly ya amsa min ya kashe wayarsaâ€?. Mu karasa a littafi na 3. Sumayyah Abdulkadir 07030137870 9/23/21, 8:19 PM - Buhainat: Suna shigowa get maigadi ya bude musu suka shiga. Tun bai gama parking ba Fahimah ta bude kofar za ta fice da niyyar ta yi ta kanta. Wannan Uwaisun bata gane masa ba da murmushin sa akai-akai. Ta sa a ranta in ta shige daki yau Uwais bai kara ganinta sai Ammi ta dawo. Amma me? Ta-yi ta-yi ta bude kofar ta ki buduwa. Ya kulle ta automatically. Juya idanu ta yi tana kallonsa da sigar tambayar dalilin kulle mata kofa. Ya wani lumshe ido a cikin kallonta. “Saurin me ki ke haka?â€? Fahimah ta dafe goshinta da ke sarawa, ta ce, “Ka san ba ni da lafiya, ina so na je na kwanta ne, don Allah ka bude min kofarâ€?. “Ba ki ji likita ya ce, I can take care of you ba? Ni kadai ke da maganin ciwonkiâ€?. Fahima ba ta san sanda ta kwalalo ido ba tana kallonsa. “Ciwo na? Wane irin ciwo ne da ni? Zazzabi fa kawai nake yi da ciwon maraâ€?. “Duk ina da maganin suâ€?. “To ba ni insha in je in kwanta, wallahi kaina sarawa yake yi, kuma kana ta sa ni maganaâ€?. “Biyo ni mu je, magungunan suna daki naâ€?. Ya saki locks din da ya kulle motar da su, wata zuciyar na cewa ta je ta karbo wata na gaya mata wayo zai yi mata, ba shi da wasu magunguna a daki, gara ma ta duba first aid box din Ammi, ba za ta rasa kowanne irin magani ba. Uwais din nan sai ta yi a hankali da shi, shegen wayonsa da son kansa ya fi karfinsa. Suna shigowa falo ta nufi dakin Ammi ba tare da ta kalle shi ba, shi kuma ya bi ta a baya, first aid box din ta nufa ta bude tana duba magungunan ciki. Sai jin Uwais ta yi a bayanta, sassanyar numfashinsa na dukan wuyanta. Sannan ya rungume ta ta baya. “Me ki ke nema ne haka?â€? Ba tare da ta juyo ba murya na rawa kamar yadda jikin ta ma ke yi, ta ce, “Maganiâ€?. “Amma na ce miki ina da su, mu je part dina in ba ki ko?â€? Fahimah ta soma hawaye, because he is dragging her closer, and he began caressing her gently, and the touches are irresistable amma haka ta jajirce ta soma kokarin kwatar kanta. “Yaya Uwais, dakin Ammi ne fa?â€?. “Abin da Ammin ke so kenan, shi ya sa ta bar min ke, ta bar mana gidan daga ni sai ke, don tana so mu zama abu guda. Na tabbata ita ta hana Talatu dawowa. Look Fah-himah, today I disregard all your clumsy excusesâ€?...". Fahimah ta wara fararen idanunta gaba daya tana kallonsa da mamaki, sannan ta kankance su cikin tsiwa ta ce, “Wallahi sai dai ka yi raping din nawa Uwais (as you earlier said), don na san ka fi ni karfi. Amma da amincewata da yardata ba zan taba bada alfarmata ga mijin da na tabbata ba ya sona ba!â€?. Tamkar wanda ta kwara wa kankara haka ya ja birki ya saketa. Tunda kuwa ta yi rantsuwa ya san da gaske take. Kwakwalwarsa gaba daya ta rikice, Fahimah na so ta zauta shi, ta yi amfani da wannan damar ta raba shi ta fice cikin hanzari. Kafin ta kai daki hawaye sun jika mata fuska; raunin diya mace, weakness na mace kan wanda ta ke matukar so, da tausayin abin da ta ke kauna, ta san da gaske yake yana cikin wani hali da yake tsananin bukatar taimakon matar sa, ita ma kuma tana bukata, Uwais ne fa! Amma da a yi 'a rashin uwa' da itaâ€? gara kowa ya mutu da urges ya huta. Ta dauka zai biyo ta, shi ne dalilin da yasa ta rufe kofar da mukulli ta kuma bar shi a jiki don ma kada ya dauko safayar na Ammi ya cigaba da damunta, amma har dare ya tsala ba ta kara jin motsin shi ba. Sau uku tana lekawa ta taga ta tabbatar yana nan bai fita ko'ina ba, ta hanyar ganin motar sa, sai ta yi ajiyar zuciya ta koma ta kwanta Amma kuma barci ya gagara zuwa ga Fahimah a wannan daren, tunanin a wane hali Uwais yake? Ya hana barcin zuwa ya kuma hana ta zaman lafiya. A daddafe garin Allh ya waye da ita, barcin da ta yi yau kwata-kwata bai yi na awanni biyu ba. Da ta tashi duk sammakon ta ba ta ga motarsa ba, tabbacin ya fice ofis ba tare da ya nemi karin kumallo daga gare ta ba. Don haka ita ma ta yi shirin shiga makaranta don bada excuse na zuwa Sudan kwana biyu ko uku ga abikan karatunta don su yi mata attendences, amma duk jikinta a sanyaye yake. Tana dai karfafa kanta da cewa hukuncin da ta zartar shi ne daidai, kada ta bari soyayya a inda ba ta da gurbi ta kassara rayuwarta. Ya jira matar SO ta dawo. Su dora daga inda suka tsaya. ***** Ta yi wanka ta shiga kicin domin nema musu abin da za su ci. Duk da ba ta da tabbas ko zai ci din? Tunda fushi yake, fushin da ta ke kira na karfin hali wai barawo da sallama. Kai da ba ka son mace, ka fada ka kara, a idonta da bayan idonta, don me ka ke son auratayya ta kasance a tsakanin ku? Haka kawai ita ma a barta stranded din idan matar so ta dawo babu gaira babu dalili? A hakan ma yaya ta kare da sabbin darussan da ya koyar da ita duk da bata san kan dawar garin ba? Ba ta taba ganin mutum mai son kansa a duniya irin Uwais ba. To ita ma tana son kanta, kuma za ta yi wa rayuwarta gatan da bata da shi in reality, sai ranar da ya furta mata hakikanin kalmar so daga zuciya da ruhi, da kuma fatar bakinsa. Ya janye mummunan sunan da yake kiranta da shi na gorin halitta "Goddam Black". Yamma lis Uwais ya shigo gidan, a matukar gajiye ya ke ga yunwa da ya dawo da ita, rabon shi da sanya wani abu a bakin shi tun wani dan hot coffee da ya sha da safe a ofis da bai fi rabin kofin mug ba, inda akwai abin da Uwais ba ya yi wa fulako ko zuciya to abinci ne, ko dazu da safe duk da fushin da yake da Fahimah kafin ya fita sai da ya duba ya ga ba ta ajiye komai ba shi ne ya fita, amma shi zai yi fushi da komai ban da cikinsa, sabida yawan excercise din da yake yi yana saka shi saurin jin yunwa. Yana shigowa dining ya nufa. Luckly ta ajiye lafiyayyar sakwara (pounded-yam) da miyan Ugu wadda ta ji naman rago zuqu-zuqu. A gefe ga jug na lemon carrots da ta hada da fresh abarba, ta zuba kananun kankara a cikin sa. "Ko da wannan mijin fahimah ya tsira ya tsira". Uwais ya ce a zuciyarsa, yana mai jan kujerar da ya saba zama akai a dining din. Ammi ta yi mata kyakkyawan raino mai matukar ban sha'awa, tarbiyya ingantacciya da kuma tsayuwa a kan ra’ayi guda. Ya fahimce ta tun jiya, ya fahimci manufarta as the same time ya kuma yaba da jarumtakar ta. Amma har gobe yana faman cigaba da lalubawa a fadar zuciyarsa bai ji tsayayyen muhalli ga Fahimah ba, balle yayi mata karya wadda ba halin sa ba. Amrah ta bi ta cike kowanne gurbi ita dai barta da son bokonta. Ta karaso wajen yana cikin cin abincin, sanye da riga da wando na Pakistan ruwan zuma, ta kame kakkarfan gashin kanta a tsakiyar kanta wanda bai da tsayi sai cika da kuma karfi na hausawan usli. Ta lulluba mayafin kayan a kanta. Idanunsu suka hadu, duk sai ta ji kunya ta kamata. Data tuna rashin arzikin data yi masa jiya. Uwais kallonta kawai yake har ta karaso, ya aje cokalin hannunsa. Ta yi wani fresh da ita, dark-skinned din sai sparkling ta ke yi. Ashe dai a can baya kallon tsoro yake mata, bakin ma, kyau ne, ga wanda ya yi dacen sa. “Ki dau abinda za ki dauka, gobe za mu wuce wajen Ammi, sai ki je ki ba ta bayani cewa kin ki yarda auren ya dore yadda ta ke so, kuma ba daga gare ni ba daga gare ki. Na yi rantsuwa da Ubangiji idan baki sauya ra'ayin ki ba har muka dawo, mata ta uku zan aura muna dawowa daga Sudanâ€?. Yana fadin haka ya ture plate din gabansa ya mike. Murmushi ya kwace wa Fahimah, beautiful serene smiles, ko mene ne damuwarta don Uwais ya kara aure? Ai kishi na matar so ne, ita ke da damuwa. Ita matar shige ina ruwanta? Ammi kuma in ya ga zai iya tarar ta ya fada mata wannan babbar maganar ai sai ya je ya gaya matan. Kaya kala biyar ta kara dauka, sai na barci da na amfani, wadanda suka dawo da su daga Lagos ta zuba su a kayan wankin ta, tana shirin kwanciya sai ga Uwais ya shigo. Ta yi maza ta maida rigar da ta ke niyyar cirewa ta canza da sleepy, ya yi kamar bai ga abin da ta yin ba, ya zauna daga tebir din jikin madubi. Pajamas ne a jikinshi farare ‘yan gidan Marks & Spencer. Bakin gashinsa sai sheki yake cikin hasken farin kwan lantarkin da ya haskake dakin. Ya ce, “Sorry, I’m not here for what you are thinking right now. Na zo ne mu fahimci juna kafin zuwan matata ta uku. Ina son sanin me ye a ranki game da ni Uwais, da har ki ka yarda aka kulla irin wannan auren tsakanin mu ba ki yi kowanne irin protest ba alhalin ba kya sonaâ€?. Fahimah ta lumshe idanunta, wai ita yau Uwais ke wa gorin ba ta son sa! Ina ma ana ciro zuciya a nuna, ta tabbata da Uwais ya yarda duk duniya babu macen da ke sonsa kamarta. Ba ta tanka masa ba ta dauki kayan da ta ke son canjawa ta yi toilet, ta sanya sannan ta fito duk Uwais na kallon ta. Ya rasa abin da ke damunsa a wannan dan tsukin a kan Fahimah da har ya biyo ta dakin ta again duk da wulakancin da ta yi masa jiya, wanda babu 'ya macen da ta taba yi masa. Alal hakika ji ya yi kawai yana son ganin ta kafin ya kwanta, ya tsokane ta ko ‘yar kokawar ce ya lakato su yi, it will keep him company tonight. “Fah- himah, ina magana shi ne ki ka yi banza da ni ko?â€? Ya fada cikin rauni, da muryar da Fahimah ta yi tantamar anya ta Uwais ce? Zama ta yi a bakin gado tana kallonsa da idanun mamaki dafe da goshin ta, kafin ta yi wani kasalallen murmushi. “Yaya Uwais ban gane tambayar taka ba ne, protest kamar yaya?â€? “Irin ki dan nuna wa Ammi rashin amincewar ki da auren, tunda kin san ba son ki nake ba, kema kuma na fahimci ba sona kike ba da baki yimin abinda kika yi jiya ba, amma sai ki ka yi shiru, aka kwaci sadaki daga mijin wata ta karfi da yaji aka baki, kuma an ce ki yi aikin sadakin kin kiâ€?...â€?. Ya fada yana kallonta kai tsaye cikin idanunta da narkakkun kwayan idanunsa. Wani kallo ne mai nuna tsananin bukatuwar miji zuwa ga matarsa.... wanda Fahimah ba ta san ma’anar sa ba. 9/23/21, 8:19 PM - Buhainat: Daga lokacin da ya taso zuwa lokacin da ya iso gare ta, Fahimah ba ta farga ba. Ta dai tsinci kanta ne a tsaye nannade cikin hannayen Uwais. And he began to kiss her, first softly, sannan gently, kafin ya maida shi a urunce (abruptly), kafin kuma ya dakata yana kallonta kasa-kasa. “Karya ki ke Fah-himah, kina sona, kina son Yayanki Uwais ba tun yau ba, bakin ki bai fada ba amma zuciya da gangar jikin sun gama confessing, na tabbata son ne kuma ya sa ki ka amince da aurena babu protest. A bisa hakan ,nake rokon ki da ki yi hakuri da ni, mu yi amfani da son da ke dankare cikin zuciyar ki mu gina kyakkyawar mu’amala ta aure. Ki manta da cewa wai bana miki so irin na soyayyah. Babu abin da lokaci ba ya canzawa Fah-himah. Ki bar ni in tabbatar da sunnar da ke tsakanin mu, na yi miki alkawarin ba za ki yi da na sanin ba ni rayuwar ki ba. Ban yi miki alkawarin SO ba, amma na yi miki alkawarin ADALCIâ€?. Wani haushi ya zo ya tokare Fahimah a kahon zucci, duk da kasalar Uwais da maganganun sa ya saukar mata, amma bacin ran kalamansa na karshe ya sa ta angije shi. Ta juya masa baya tana hawaye. “Yaya Uwais ka fita min a daki, pls, tunda ni da bakina ban furta maka kalmar so ba, don Allah ka daina furtan kiyayya. Babu adalcin da nake bukata daga gare ka duk ka hada ka baiwa matar so. Ina bukatar sarari wallahi, kasa daki na ya min kadan, kana sa min ciwon zuciyaâ€?. Uwais ya zuba hannayen shi duka biyu cikin aljihu yana kallonta da murmushi a siririyar fatar bakinsa. “Then why are you jeolous? Da matar so da wadda za a karo?â€? Da sauri ta juyo, ba ta san ya karaso bayanta ba don haka kanta ya bigi kirjinsa. Ta sake ja da baya ta ce, “Kishi kamar ya ya fa? Ban gane ba? Na ce kar ka yi aure, ko na ce kar ka koma wajen matar ka?â€? “But you called her MATAR SOâ€? in ba kishi ki ke ba don me za ki kira ta da wannan sunan?â€? Fahimah ta gama lura tsab yau Ya Uwais neman magana ya ke ji, ya zo ne musamman don ya yi ta takalar ta, tayi ta hargagi yana murmushin jin dadi, ta fahimci in za su kwana suna yi ba zai gaji ba. Sai kawai ta yi tattaki da baya-da baya ta shige toilet da sauri ta murza key ta barshi a wurin. Uwais ya karaso kofar toilet din ya ce, “Ni ki ka kulle wa kofa Fah-himah? Ai ba sai kin kulle ba na gaya miki tun shigowa ta I’m not here for what you are thinking. Na zo ne mu fahimci juna, kuma alhmdulillah na gama fahimtar duk abin da nake son fahimta a kan ki. Ya rage naki ki baiwa zuciyar ki salama da abin da ta ke so, ko ki yi ta zaman jiran tsammanin warabbuka (sai ranar da aka so ki kamar matar so). Ci ba daya ba kuwa, ai koshi bai taba zama dayaâ€?. Fahimah ba ta tanka sa ba, ta san ta shaka masa. A yadda ta ganshin nan da bata tsere ba abinda zai biyo baya Allah kadai ya sani. Ta ganshi ya koma kamar ranar su ta farko a Lagos. Rabar da period ne kadai ya ceceta. Tsoronta daya ne kada ya fita neman matan kan titin kamar yadda yake ikirari, don haka ta yi ta leke ta tagar bandakin ta tabbatar motarsa tana nan bai fita ba. Ta yi ajiyar zuciya ta fito ta rufe dakin ta ciki, sannan ta yi alwallah ta kwanta. Ta kasa barci, sai tunanin maganganun Uwais dalla-dalla. A zahiri ta gane cewa; their relationship is taking another direction. Ta tuno yadda Uwais yake kissing nata a Ikko da dazu babu kyama, a hakan ma don tana zamewa ta ki sakar masa jiki. It was all sudden changes a tare da shi wadanda bata taba tsammanin za su faru da shi ba cikin dan kankanin lokaci irin haka. Sai dai ta lura shi a karan kansa bai san da wadannan tarin sauyukan a tare da shi ba. Da ma an ce mahakurci mawadaci, kuma mai hakuri shi ya kan dafa dutse har ya sha romon sa. Idan tafiyar su ta ci gaba a haka, ba ta san iya ina za ta kai su ba, amma dai ko ina ne destination din zai zamanto mai ma’ana ne. Me ya kamata ta yi maimakon kwanciya? Ai kawai ta tashi ta gode wa Sarki Allah. Jallah Wa Azza. Wanda cikin mulkinSa da buwayarSa ne yake ta karkato mata da zuciyar Uwais, batare da shi din ya san hakan ce ke faruwa da shi ba. All of a sudden, da ma dai Ammi ta fada, “Uwais bai iya rayuwa ba tare da mace ba", kuma ga zahiri tana ta gani. **** Uwais da Fahimah, washegari a cikin jirgin SUDAN AIRWAYS, wannan karon bai kai ta economy class ba, ya barta a first class seats kusa da shi duk da cewa ya ki sakar mata fuska sabida abinda ta kara yi masa daren jiya. Tun da suka taho yake kumburi, ga wani bakin dark spaces ya maka wa kwayar idonsa, wanda ya boye halin da kwayar idanunsa ke ciki. Ko abincin da aka ba su a jirgi bai taba ba, duk a cikin fushi ne, fushi yake sadidan da Fahimah, ita kuwa ko a jikinta. Ta ci abincinta ta yi nak! Aka zo aka kwashe kayan, ta soma jin barci, sai ta jingina da kujerar sa barci ya dauke ta. Ba ta san ya ya aka yi ba, ta farka ne ta ganta kan kafadun Uwais tana barci. Ko ita ta sulmiyo zuwa jikinsa, ko shi ya gyara mata kwanciyar ba ta sani ba. Da asubahi suka sauka a Khartoum babban birnin kasar Sudan kuma garin su Ammi, Mahdi babban dan Baffa Shuraim shi ya zo ya tafi da su zuwa can main house din su Ammi, inda a can ne ake zaman makoki. Ammi baki ya ki rufo, da ganin yadda Fahimah ta yi mulmul cikin 'yan kwanaki kalilan. Wannan ya tabbatar mata suna cikin kwanciyar hankali fiye da tunaninta. Duk da an yi addu’ar bakwai an watse dangin Ammi na nan ba su koma ba, nan ta yi ta gabatar da Fahimah matsayin ‘yar ta da ta rike tun tana karama kuma matar Uwais. Wasu sun yaba, masu racism din ciki ba su yaba ba, kin san balarabe da kabilanci. Matar Mahdi sai da ta yi gulmar Ammi a bayan idonta ta ce da mijinta Mahdi cikin harshen larabci, “Duk matan Sudan Ammi Safeeyyah ta rasa wadda za ta aura wa Uwais sai mara asali mara hasken fata?â€? Mahdi ya harareta yace "to ina ruwan ki? Ita ta ga tayi dai-dai da danta, ko ke kika haifa mata shi?" Da yawa kuma tarin nutsuwar Fahimah da rashin rawar kanta, uwa uba kwarjinin da Ubangiji ya yi mata shi ya burge su zuciyar su ta kaunace ta. Da daddare Uwais ya shigo yi wa Ammi sallama zai tafi masaukin shi ya kwanta, Mahdi na jiransa a waje cikin motarsa zai sauke shi. Sannan ya wuce nasa gidan. Fahimah na gefen Ammi tana cin abincin dare sanda Uwais ya shigo. Kallo daya ta yi masa ta dauke kai, shi ma ya yi kamar bai ganta ba, amma gani ta yi har duhu ya dan yi sabida gajiyar da ke tare da shi. “Ammi fi-amanallah zan je na kwantaâ€?. Ammi ta ce, “Allah ya huta gajiya, a ina ku ka sauke shi Mahdi?â€? Mahdi ya ce, “Nan gidan saukar bakin Abbu na gyara masa daki, amma shi ya ce ya fi son Fundaq (hotel)â€?. Ammi ta dubi Fahimah da ta kasa ci gaba da cin abincin ta ce, “Sai ki tashi ku tafi, ni ba zan kwana gado daya da ke ba, hauri ki ke yi da wadannan dogayen kafafun naki in kina barciâ€?. Fahimah ta zaro ido tana kallon Ammi. Uwais bai ce komai ba ya juya ya fita, yanzu sai ta tsallake kowa da ke cikin gidan nan ta bi Uwais zuwa masauki? Ta bude baki za ta yi magana, Ammi ta jefa mata mayafin ta ce, “Do as I saidâ€?. Tana kunkuni hadi da turo baki gaba ta mike, “Duk mutanen gidan nan Ammi?â€? Ammi ta ce, “Su ba a dakin mazan su suke ba? Bari mu koma gida da ni ki ke zancen, wallahi tarewa za ki yi ko kuma ya dawo da matarsa, ba zan dauki rainin hankali ba, ku zo ku sa ni a tsakiya ina dalili ni ba tsohuwar banza ba?â€? Tuni Fahimah ta kai kofa, ga uban horn da Uwais ke antayo mata don ya tsani jira a rayuwarsa. Suna kan hanya shi da Mahdi da ke tukin mota suna gaba, ita kadai tana gidan baya. Uwais ya yi kwafa sannan ya yi magana da hausar da ya san Mahdi bai ji. “Da ma kin dage kin ki biyo ni, a’a ke komai sai ki yi shiru ke ga sarkin biyayya wa Ammi, in kin biyo ni amfanin me kike amfana min? To ni zama da ni DEAL ne kin sani, gara ma ki rufa wa kanki asiri ki bi Mahdi ku komaâ€?. Fahimah ba ta tanka shi ba. Daidai lokacin da Mahdi ya shigar da mota hotel din, shi ya je ya yi musu komai, sannan suka haura dakinsu ta elavator. Suna shiga dakin wanka ta shiga ta fara yi sabida tunda suka iso ba ta yi ba, jikinta har danko-danko yake mata, sanda ta fito Uwais na kishingide cikin kujera ya yi rub-da-ciki yana waya. Daga yadda yake magana kasa-kasa da tausasa murya ta fahimci shi da matarsa ne. Sun gama fadan kuma sun shirya. Maganganun da ta ji ana yi cikin wayar sun girmi kwakwalwarta, don haka ta ga gara ta fita ta ba su fili kafin ta samu heart attack. Uwais har da gayya yake fadin, “Zan iya hakuri mana Amrah? Amma na kwana arba’in, daga nan duk ‘yar akwalar da na samu zan yi maneji da ita, da yardar ki ko babu, kada ki ga laifina in ki ka dawo ki ka same ni da sabon aure…â€?. 9/23/21, 8:19 PM - Buhainat: Murjanatu ta ce, "Ki yi wa mijinki kyakkyawan zato Amrah, Uwais mutumin kirki ne a fili da boye as far as i know, bana zarginsa da wannan. Amma lallai ne Amrah in kina son aurenki ya dore, kuma martabarki ta dore a idon Uwais to ki sake shawara a kan karatun ki. Tunda ya fito fili ya nuna miki ba zai iya hakuri ba, bana jiye miki matan waje don Uwais ba irin nasu bane. Amma ina jiye miki kishiya da kuruciyar ki…â€?. Gaban Amrah ya yi bala’in yankewa ya fadi da kalaman Murjanatu na karshe, wani abu da ba za ta taba iya yarda da shi ba (tarayya da wata a kan Uwais), gara mata ranar mutuwar ta da ganin wannan ranar. Amrah ta dubi Antin ta Murja cikin karaya, ta ce, “Aunty Murja, ba ni ce abun ji ba, Daddy ne, kuma dai kin san yadda karatun likita yake a kasar nan sai ka yi shekaru goma ma ba su sallame ka ba, sannan gaskiyar magana Uwais yana da takura, mayata har da hayyata. Tafiyata na dan lokaci ba ki ji hutawar da na yi ba da sararawar da na yi. Sannan ni ba zan iya karatu a Kano ba, gaskiya na riga na saba da Malaysiaâ€?. Aunty Murja ta ce, “To Bamaleshiya, haifaffar Malay, sai kuwa ki baiwa Uwais dama ya yi aure shi ne kadai mafita ga matsalolin kuâ€?. Amrah ta kankance ido tana duban Murjanatu, ta ce, "Over my dead body!". Murjanatu ta ce, "Ki daina fadin haka kada ki fada da bakin Mala'iku Amrah, kuma ki mutun, a zo a yi, gara ma a yi kina rayen, kowacce ta murza kambunta, in ya so wadda ta fi son mijin ta kwace, don ina tantamar soyayyar ki ga Uwais idan ba ta fi cikin cokali ba. Ki yarda kin fi muhimmanta karatu da aure Amrah. Sannan kina son kan ki da yawa, kuma irin ku masu gudun kishiya an fi yi muku wallahi". Maganganun Murja sun ki yi mata dadi ko kankami, domin Murjanatu irin mutanen nan ne masu tsage gaskiya komai dacinta. Don haka Amrah ta tashi ta bar mata falon tana kunkuni, cikin kunkunin fadin ta ke, "Aunty Murja ba ta sonta, tunda ta ke mata fatan kishiya". Murjanatu ta bi ta da kallo cike da tausayinta, ta san upbringing na gidansu shi ne babban abinda yake wahalar da ita, ita ma haka ta sha wahala da Jabeer don shi cewa ya yi ko haihuwa ba za su fara ba sai sun yi shekara goma da aure. So many challenges ta fuskance su a kan Jabeer irin na Amrah a kan tsananin bokon su. Farkon aurensu ko sallar asubah sai ya gama shirin ofis yake yinta don kada ya makara ofis. Sai da ta dage wajen kyautatawa da lallashi cikin hikima ya koma yarda ta tada shi sallar asubah. Amma har yanzu in yana wasu abubuwan za ka fahimci sun fi bai wa boko muhimmanci a kan addini. Tana tausaya wa Amrah, musamman da ta fahimci weakness din mijinta, kwace mata shi daga wajen sauran mata na ciki ko na waje ba zai zamo abu mai wahala ba. Wai Hausawa suka ce kwace goruba a hannun kuturu ba wahala...... **** KHARTOUM Ammi ce ta kira wayar Uwais ganin shiru-shiru har azahar ba su ba alamar su a main house. Ga shi Mahdi ya ce mata Fahimah ce ba ta jin dadi, don haka hankalinta ya ki kwanciya sam. Uwais na dagawa, ta ce, "Ya ya jikin Fahimah? Ko dai a kawo ni mu je asibiti?" Uwais ya shafo lallausar sumar kansa cikin jin nauyi, ya ce, "Ammi ta wartsake fah, wanka ma ta ke yi yanzun, muna nan tafe zuwa karfe hudu". Ammi ta ce, "To alhamdu lillah, abinci fa?" Uwais ya ce, "Kada ki damu Ammi na yi order a nan an kawo mana tun dazun". Hawayen farin ciki suka cicciko a idon Ammi, don ta gama gane ciwon na Fahimah ta ce, "Allah ya yi muku albarka Uwais, Allah ya jikan mahaifinka, yadda ka yi min biyayya Allah ya ba ka masu yi maka, yadda ka faranta min kai ma Allah ya faranta maka". Tunda yake da Ammi ba ta taba yi masa addu'ar da ya ji dadi, kuma mai tsayi kamar wannan ba. Ko don ya ci gaba da samun wannan tofin albarkar ya yi alkawarin rike auren Fahimah da amana da hannaye bibbiyu. A ransa fadi ya ke, "Ammi ai gata ki ka yi mun, you gave me a precious gem, wanda ba zan gushe ba ina nema miki rahmar Ubangiji da gafarar sa a kansa. Fahimah ta fito daga toilet, ta yi wanka amma ta dauko kayan da ta tube ta maka, kasancewar ta manta bata shiga da wadanda za ta canza ba, kuma ba za ta iya fitowa daure da tawul a gaban Uwais ba. Ya daga lumsassun idanunsa yana kallonta, her radiant black skin sai wani sheki ta ke kamar ta matan kasar Ghana, ta wani fannin kuma Somalis. Ta fiddo doguwar riga ruwan makuba kirar Dammam daga cikin kayan ta za ta saka, ba ta san lokacin da Uwais ya taso ya iso gabanta ba. Fuskarta da ruwa bai iya zama sosai sabida santsinta ya dan shafo, sannan ya hau kici-kicin cire mata rigar da ta mako. "Ya Uwais lafiya?" Ta fada cikin kidima, don yanzu Uwais ya zame mata dodo. Yesterday night will forever remain fresh in her memory kuma bazata gushe ba tana tuno komai da ya wakana cikin daren ba a duk lokacin da Uwais ya kusance ta. Cikin kokarin kwantar mata da hankali da rage mata karfin tsoron da ya gani cikin idanun ta a kansa ya tausasa murya ya ce. "Nothing as you expect, daga nan har dare kina da hutu, kawai kayan zan canza miki da kaina don ki sani yanzu ke da Uwais, babu sauran shamaki, ki daina wannan nukunukun na canza kaya a gaba na". Fahimah ta runtse idanunta a lokacin da Uwais ya fidda rigar jikinta gabadaya ta saman kanta, ya tsura mata idanu yana tazbihi ga mahaliccinsa. Ya juyo ta round sannan ya rungume ta. He then began to kiss her passionately, al'amarin da bai tuke a ko'ina ba sai a tsakiyar gadon barcin su. Hutun da bata samu ba kenan saidai wannan karon bata ji wahalar da tayi tsammani ba, ya tafiyar da komai gently cikin nutsuwa da soyayya. Ba su suka tafi gidan su Ammi ba sai karfe biyar na yamma. Ammi girki na musamman ta yi wa Fahimah da kanta, farfesun Zabuwa da ya sha kayan kamshin larabawan Sudan, sannan kunun kanwa mai yaji da zafin sa, ta sa ta a gaba ta ce sai ta shanye, kuma yanka daya ba za ta bari ba. Ba su kara ganin Uwais ba sai karfe tara na dare, don sun je Oumdurman gaida wani kakan Ammi. Yana shigowa dakin da suke da sallama dauke a bakin sa bayan dawowar su daga Oumdurman. Fahimah ta kara mannewa ta lafe a jikin Ammi gabanta har lugulgude yake. Soyayya kam ta ci gidansu, bata marmarin komai yanzu banda isashshen barci, yanzu Uwaisun kam shi da dodo ba su da maraba a idon Fahimah. Ammi ta ce, "Har an dawo? Ya ya ku ka baro mutanen Omdourman din?" "Kowa lafiya Ammi duk suna gaishe ki, na gaji sosai Ammi, Oundurman akwai nisa". Ammi ta dubi Fahimah da ta bingire a kasa tana barci. Ta ce, "Ke kuma Fahimah barci haka kamar 'yar goye muna hirar mu yanzun nan?" Uwais ya yi wani miskilin murmushi don ya san barcin karya ne Fahimah ke yi. Ammi ta soma bubbuga ta, "Fahimah-Fahimah, tashi mana ku tafi?" Fahimah ta tashi tana mutsittsikar ido da turo baki ta ce, "Ammi ni a nan zan kwana, wallahi Ammi ban iya takawa na gaji". Uwais ya kanne ido guda a gaban Ammi, ya ce, "Ba matsala, sai in dauke ki don dai zuwa mota?" Kunya ta kama su daga ita har Ammin sai da ta yi da-na-sanin karyar ta, ya mike yana fadin, "Ammi bar abincin nan, mun ci a Oumdurman. Idon na fita kuma, zan sha fresh milk a Fundaq". Ammi ta ce, "Tashi ku tafi Fahimah kin ji? Kin ga gobe za ku koma gida akwai bukatar ki tattaro kayan ki da kan ki, kada ya manta miki wani abu. Amma Fahimah fir ta ki tashi, Ammi so ta ke Yaya Uwais ya karasa kashe ta da ranta, saboda cikin al'amarinsa babu daga kafa babu tausayi ko jin lallashi. Ammi ta kada ta raya amma Fahimah ta kafe abinda bata taba yi wa Ammi ba (musu) ta ce ita kam ta zo kenan, Nigeria ma ba ta komawa sai tare da Ammi. Ya dauko mata abinda zai iya ya bar ragowar. Tausayi ya sa Ammi ta kyale ta, ta kira Uwais wanda har ya shiga mota ta ce su tafi su bar ta, ya taho mata da dukkan kayanta. Za ta lallaba ta gobe su koma gida tare. Bai ce komai ba amma ya hassala, ya ce da Mahdi ya ja motar su tafi. Cikin daren kuma Ammi ta dauki lokaci tana nusar da Fahimah akan aure, ta ce, "Wannan shi ne ai auren Fahimah da manufar yin sa. Hakuri da juriya za ki sa a ranki, duk wata mace da ki ka gani da 'ya'yanta abin sha'awa sai dai ta yi wannan hakurin ta same su. A hankali za ki saba kin ji ko Fahimah ta? Lada ne babba ki ke samu a wurin Ubangiji wanda zai miki silar shiga aljannah". Sosai ta fahimci cewa cikin al'amarin Ammi Safeeyyah babu son kai ko son zuciya, face kauna zallah ta fisabilillah da ta ke mata, shi ya sa ta ke so mata rayuwa da gudan jininta mafi soyuwa a gare ta. Fahimah ta kwana addu'ar Allah ya ba ta lafiya, juriya da tsawon ran da za ta ci gaba da kulawa da bukatar gangar jikin Uwais, da komai nasa, har zuwa ranar da ta daina numfashi. ****** Washegari suka yi sallama da kowa, bayan Ammi ta tsuma 'yarta ta gyare ta tas da gyara irin nasu na Sudanese din asali. Jirgin karfe tara na safe suka biyo wanda zai sauka a Kano. A cikin jirgi babu irin korafin da Fahimah ba ta sha daga Uwais ba a kan abin da ta yi masa jiya, har da cewa, "Me ki ka dauke ni ne? Wanda bai iya rayuwa sai da ke ko me? Dana kwana nikadai me kika ga ya same ni? Karewa ma matata da na ke so ta dawo already, don ta bani kulawar da duk nake bukata. Don Allah Fah-himah ki jika abinki ki shanye". Fahimah ba ta tanka shi ba, amma ji ta yi gaba daya hankalinta ya tashi. Idan da gaske Amrah ta dawo ita mene ne makomar rayuwarta? Shin za ta iya sake barci a duniya ba tare da Uwais a gefenta ba? Ya sanya ta cikin wata sabuwar rayuwa mai wuyar bari da wuyar mantawa. Ta yarda ashe a can baya So kawai ta ke masa na fatar baki, yanzu ne ta san tana son Uwais har ruhi da bargon jikinta. Idan kuwa abin da Ammi ta ce gaskiya ne (physical relationship between husband & wife). Alamu ne na so, kuma ba ya faruwa sai da soyayya ko yaya ne, to ta yarda Uwais yana sonta ko da bai furta a fatar bakinsa ba. Ita kam ai yanzu kalmar kiyayyar Uwais ta daina razana ta, ta daina bakanta mata rai ko da zai kwana yana fadi akan mumbari ta bakin Ammi, domin kuwa har kakannin I love you Uwais ya gaya mata ba tare da ya san lokacin da ya fada din ba. In haka ne ashe ita ma mutum ce, kuma mace mai daraja kamar kowacce mace duk da kalar fatar tata, ba za ta kara bar wa Amrah miji ita kadai ba. Da Uwais ya ishe ta da mita da korafinsa da ya ki karewa sai ta tashi tsam ta bar masa wajen, ta koma can wata empty seat a cikin jirgin ta zauna. Tunda ya ambaci cewa Amrah ta dawo ta ji ko muryarsa ba ta son ji, kallonsa ma bacin rai yake sanya mata. Ya so ya bi ta inda ta koma ya ci gaba da damunta da complain don kuwa ba da wasa ba ya azabtu a jiyan, ya ji haushin abinda tayi masa, yayi hakuri ne sabida Ammi, sai ya hango ta tana share hawaye, duk kuma sai jikinsa ya yi sanyi, domin ya fahimci ko me Fahimah ta ke wa kuka ba zai wuce RABUWAR SU ba tunda Amrah ta dawo. To amma shin yana da guts na gaya wa Amrah yana da wani auren, auren ma na wadda ya taba kira ‘yar aikin gidansu? Ko kuwa shin zai iya jure rayuwa yanzu babu Fahimah? Tsakanin ita da Amrah wacece ta fi muhimmanci ga rayuwar sa? Tambayoyi ne da ba shi da amsarsu, kuma bai san amsar tasu ba. Sannan bashi da mai amsa masa. Har jirgin su ya yi landing a Kano. A nan airport dama ya adana motarsa, ya je inda ya bada ajiyar ya dauka suka wuto gida. Baba Talatu ce ta bude kofar falo tana musu sannu da zuwa, ta karbi kayayyakin hannunsu, Uwais ya wuce bangarensa, ita ma sai ta wuce nata dakin domin ta yi wanka ko ta warware gajiyar da ke nukurkusarta. Kafin ta fito Baba Talatu ta shirya musu abinci a dining mai rai da motsi, wanda ta yi musamman domin tarbar su, sinasir ne da waina da miyar egusi wadda ta ji ganyen alayyahu da naman rago. Fahimah sai ta samu kanta da zama ta tsantsara kwalliya ta gani ta fada da kyakkyawar atamfa super Vlisco light blue. Wai aka ce in ba ka yi ba ni wuri, ba za ta kara bari a barta matsayin ‘yar jiran gida ba. Uwais ya fito bayan magriba ya canza zuwa kananan kaya, bakar riga ce shirt a jikinsa samfurin Balanciaga da wando chinose, sumar nan ta sha wanki da arganavita ta kara baki sai sheki ta ke. Da Fahimah ta daga ido ta dube shi sai da tsigar jikinta gabadaya ta tashi. Da ta tuna duka wannan kwalliyar ta Amrah ce ba tata ba, sai bacin ran duniya da wani bala’e’en kishi suka zo suka lullube ta. Uwais gab da ita ya ja kujera ya zauna, kafadunsu na gugar na juna, sanyin kamshin (Maison Francis) har cikin ruhinta. Ta lumshe ido sannan ta bude su a kanshi tana kallon sa da idanun rauni, jin yana take mata yatsun kafa da nashi yatsun. Ya ce, “Madame, ya ya kin gama shiryawa? Yanzu za mu wuce faâ€?. Fahima ta zaro sparkling eyes dinta a kanshi cikin rashin fahimta, Uwais ya gyada kai cikin tabbatar mata. “Tare za mu tafi Fahimah, gidanki za ki koma!â€?. Sai ta ji tamkar an yi mata rahma, duk da bata da niyyar bin nasa, at least ya nuna yana son zama da ita koda bata bishi ba, tamkar ya yaye mata wani nannuyan dutse daga kirjin ta, duk wata damuwa da wani bacin rai sai ya kau. Ta ji kamar ta rungume Uwais, amma ta kwabi kanta da ta ja ajinta. Girgiza kai ta yi, “Babu inda za ni Yaya Uwais babu sanin Ammiâ€?. Uwais ya juyo sosai ya sanya fuskar Fahimah cikin tafukansa biyu, ya sumbaci lebunanta keenly, skyblue kwalliyartacikin atampa ta yi mishi kyau ba dan kadan ba, ta kara fiddo da ainahin kalar fatarta mai kyau da ilhamar ta. Ya ce, “Idan kuma Ammin ta dawo ta ce na barki ke kadai fa?â€? Da sauri ta ce, “Ba komai, zan zauna, ai ga Baba Talatu ta dawoâ€?. “Are you sure za ki iya barci?â€? “Sure, I wouldâ€?. Sai ga hawaye kuma sun zubo. Uwais ya sanya babbar dan yatsansa ya lakato hawayen, ya ce, “Wannan fa na mene ne?â€? 9/23/21, 8:19 PM - Buhainat: Uwais ne a gaba, Fahimah na biye da shi a baya suka ratsa ta tsararrun falullukan Amrah, a falo na karshe ya ce ta zauna don yana kyautata zaton Amrah ta yi barci. Amma da ya daga labulen bedroom dinta sai ya same ta tana sallah, wadda bai san ta nafila ce ko isha ce ba. Ya zauna a gefen gadonta har ta idar. Tun tana sallar ya fahimci ta kai hannu ta toshe hanci, tsaki ya yi ya ce, “Amrah why? Wai a kanki aka fara ciki ne? ko ko naki ne ya fi na kowa tsurfa?â€? Ta sallame sallarta tana kallonshi cikin haushi, ya je ya dade ya yi dare son ransa kuma ya zo yana mata zancen wofi, zuciyar mai ciki da ma a kusa ta ke, ta ce, “Don Allah fita min a nan Uwais, da kai da gallababben turarenkaâ€?. Yau Uwais din tsura ta fada not Habiby ko Habib-Qalby, ya ce, “To kin sa na dauko ‘yar Ammi ko in maida ta ne?â€? Da sauri ta mike tana fadin, “Ai ban san tare ku ke ba, ba ka yi min bayani baâ€?. Suka tadda Fahimah a inda ya barta, Amrah da fara’a sosai ta ke mata barka da zuwa, ta dauki jakar kayanta ta ce, “Habiby ya ya sunanta?â€? Irin kallon da ya yi wa Fahimah ya sa ba shiri ta sunkuyar da kanta. Ya ce, “Tambaye ta mana? Ai tana jinkiâ€?. Murmushi Fahimah ta yi ta dubi Amrah wadda a take ta ji Allah ya dauke mata kishin Amrah da ke ranta. Ta ce, “Sunana Fahimah. Wasu kuma kan ce, Fah-himahâ€? (tana nufin Uwais, shi ne mai kiranta da Fah-himah)â€?. “Ni ma Fah-himah zan ce, yafi dadi, Fahhimah please taso mu je in raka ki dakin da na ware miki tun safe. Ki kwanta ki hutaâ€?. Fahimah ta mike ta bi bayan ta. Uwais ya bi su da kallo admiringly a zuciyarsa kuma yana taraddadin ranar da gaskiya za ta bayyana ga Amrah, duk sunan da ta kira shi da shi a lokacin daidai ne. Makaryaci? Maha’inci, mayaudari ko maciyin amanar soyayyah? He’s ready to face and accept all the names in dai a karshe za ta yi hakuri su hada kai su yi rayuwa mai albarka su ukun. Amrah will never be enough for him shi ya sani, duk da cewa har gobe ita ce zabin zuciyarsa, muhallin da kowacce ke da shi a yanzu cikin ransa daban ne da na ‘yar uwarta; duka yana son abinsa, kowacce da bigiren da ta cike cikin zuciya, ruhi da gangar jikinsa. Amma Fahimah na da wani extra matsayin a zuciyarsa wanda ya wuce soyayyahâ€? wanda sexual bond ke karawa tsakanin miji da mata, sama da wannan ita din abin so ce ga mahaifiyarsa da ba ya hada ta da kowa a duniya sannan ta zama wani babban bangare na barin jikinsaâ€? abin nufi, a ita ne yake samun nutsuwar da duk da namiji ke son samu a diya mace. Yayin da Amrah har gobe take a matsayin MATAR SO ta likawa a goshi. Ya yi kokarin ya daidaita matsayin kowacce da na ‘yar uwarta cikin zuciyarsa a daren yau, sai ya ga cewa daidaiton bai yiwuwa, domin ratar da ke a tsakani mai tsananin fadi da girma ce da ta shallake tunaninsaâ€?....Ashe namiji kan iya son wata a lokaci guda, sama da first love dinsa??? Amrah na can tana sharar barci ta yi daidai a kan gado ta baro Uwais kamar marayan da ya rasa uwa don ta roke shi kada ya zo inda ta ke in ba so yake ta amayar da ‘yan hanjinta ba. Uwais ya mike tsam yana daure igiyar pajamas din shi cikin ransa yake fadin, “Ana me? Ni ba aminin gwauro ba?" Dakin Fahimah ya nufa bayan ya leka Amrah ya tabbatar ta yi nisa a barcinta. Kamar Fahimah ta san haka za ta faru don ta gama gane Uwaisun nasu cikin dan lokaci kalilan, kunya bata ishe shi ba a wannan fannin kam, zai iya janyo mata abin kunya wajen wadda ta dauke ta 'yar uwa, don haka tun sanda zata kwanta ta rufe kofarta ta ciki da key ta kuma barshi a jiki ta yadda ko ya sa nasa ba zai shiga ba. Ya murda kofar sai ya ji ta gam-gam, wato ya ji ta a rufe, sai ya soma kiranta a matukar tausashe. “Fah-himah, bude min kofar mana, ni ne Uwaisâ€?. Fahimah da ke bisa darduma tana sallolin nafilah don gusar da birbishin kishin da ya cika zuciyarta ta yi sallama, sannan ta matsa jikin kofar cikin damuwa ta ce, “Wani abu ka ke so Ya Uwais?â€? “Ki bude na ce, ko ma me ye sai ki jiâ€?. “Gaskiya ba zan bude ba Ya Uwais". Ransa ba karamin baci ya yi ba, kuma yana tsoron ya daga murya Amrah ta tashi don haka ya sassauta murya ya ce, “Please Fahhimahâ€? I’m begging you in the name of Allahâ€?...â€?. Muryar Uwais dake raurawa har cikin tsokar zuciyarta, yadda muryar ke raurawa haka zuciyar ta ke raurawa, weakness na wanda kake so ba karamin rauni bane a gareka, amma ta gwammace ta tsaya a kan gaskiya da adalci, in ita aka yi wa haka ya ya za ta ji? Amrah ba ta san da komai a tsakaninsu ba, sai kokarin kyautata mata ta ke da zuciyarta daya. Ta dauketa kamar kanwar Uwais da ta kawo mata ziyara. Amma sai ta saka mata da dauke Uwais a cikin dakin ta? “Yaya Uwais ka yi hakuri ba fa zan bude ba. Don ban ga abin da ka ke so a nan baâ€?..â€?. Muryarsa wani iri don tsananin bacin rai, ya ce, “Fah-himah...., amma saboda takaici sai ya kasa karasawa, ya juya ya bar wurin. Dakin Amrah ya koma yana fadin yau sai dai turarensa ya sumar da Amrah in ma suman za ta yi. Fahimah ba ta san ya suka kare shi da matarsa ba, da asubah Amrah ta hau buga mata kofa, da Fahimah ta ji muryarta sai ta bude, Amrah ta fado dakin tana ajiyar zuciya, at last she escaped! Smell din da bata so. Sannan ta zauna a gefen gadon da Fahimah ta tashi, ta ce, “Zan kwanta a nan don Allah, bana son turaren Habiby, shi kuma ya ki fahimtata ya nisance ni ba da gangan nake yi baâ€?". Ta yi ajiyar zuciya abin tausayi, sannan ta dubi Fahimah cikin rauni "kin huta da ba'a yi miki aure ba Fahhimah, aure takura ne, nauyi ne, jidali ne wallahi ina da na sanin yinsa…â€?. Fahimah ta ce, “Kul! Amrah ki daina fadin haka, domin aure umarnin Ubangiji ne kuma sunnar Annabi SAW ne. Ya kuma ce wanda ba ya son sunna ta, to ba ya tare da niâ€?. Amrah ta ce, “Astagfirullahâ€? wa'a tubu ilaih, amma duk bayanin da zan miki bazaki gane ba tunda baki da aure, my husband mai yawan takurawa ne, yayin da ni nake tsaa-tsaki, sannan ina fama da kaina, amma ya kasa daga mun kafa ya bar ni in sarara ko kadan. Yanzu kam na yarda gara ya kara aure, Fah-himah I so much like you, in da aure tsakanin ki da Habiby don Allah ki taimake ni ki aure shi... tafiyarmu ni da shi ba za ta yi tsayi ba in aka cigaba a hakaâ€?...don bani da isashshen lokacin sa, yanzu haka na baro komai dake gabana na taho tun daga Malaysia don in ba shi lokacina amma na kasa faranta masa da komai, tunda na zo lafiyata ta ki daidaito. Shi kuma ya kasa daga min kafa, jiya fada muka yi baram-baram ko barcin kirki yau ban iya na yi ba…â€?. Fahimah ta rungumo Amrah a jikinta cikin lallashi, ta ce, “Ki yi hakuri Amrah, marriage is not a bed of roses kuma duk soyayya sai ana samun misunderstandingsâ€? amma Yaya Uwais is a nice person, duk da ba ni da experience a kan aure na san abubuwan da ki ke fama da su lalurorin karamin ciki ne kawai, da zarar kin samu lafiya ko kusa bazaki so kowa ya rabi Uwaisun ki ba, balle kiyiwa kan ki fatan ya kara aure, kuma insha Allah zai wuce, da zarar cikinki ya yi kwariâ€?. Ta yi shiru sannan cikin murmushi, ta ce. “Amrah ki ke so ko in ce ki ke fatan wata ta auri Uwais? Ba kya tsoron ta kwace miki shi ne? Ki bar wannan tunanin wahalar ovulation ke damunki, da kin haihu ko kuda ba za ki so ya gifta a tsakaninku baâ€?. Amrah dai ba ta ce komai ba, amma ta ji dadin maganganun Fahimah, ba ta san sanda ta fada ba tsabar bata cikin normal hayyacin ta, kuma tana bukatar taimako daga 'yar uwarta mace koda da shawarar fatar baki ne. Tace. "Fah-himah I just like you, and i love your simplicity ". Da sauri fahimah ta girgiza kai tana jin kamar ta bude baki ta gaya mata gaskiya, don ba ta saba rashin gaskiya a rayuwarta ba sam sai yau. Yau din ma don kada ta shiga hurumin da ba nata bane. Kamar Uwais ya san me ta ke shirin yi sai kawai ya bude kofar ya shigo dakin babu zaton su. Ya dau wankansa as usual ya yi shirin ofis cikin bakaken suit, ya dube su ya girgiza kai. “Daga ganin wannan zaman naku gulmata ake, kin bar ni zan fita ban ci komai baâ€?. Ya fada yana kallon Amrah directly cikin idanunta. Ji ya yi ya kara sonta duk flaws dinta, tunda tana son Fahimar sa. Fahimah sai ta zame jiki ta bar musu dakin, kofar da ta ke da tabbacin kitchen ce can ta nufa. A gurguje ta dama wa Uwais custard ta zuba madara (peak) ta ruwa gwangwani daya, ta soya plaintain da sauri ta zo ta aje masa a dining. Daidai lokacin suka fito daga dakin nata shi da Amrah, ya ja kujera ya zauna ya soma tsiyaya vanilla custard din a kofin mug na tangaran. Fahimah ba ta tsaya tare da su ba, ta koma kitchen din don ta sama wa Amrah wani abu mai dan gishiri da maggi kuma mai yaji da za ta iya ci kamar yadda ta gaya mata cewa abu mai yaji da maggi kawai taje iya ci.. Farfesun tarwada ta yi mata, Amrah ta ce ta saka tarugu sosai. Haka ta yi ta shan romon da cokali tana gumi tana fyace hanci. Da rana girki na musamman Fahimah ta yi wa Uwais tuwon semo miyan danyen kubewa da yaji zallar tsokar kaza, ta cire duka kasusuwan ta dagargaza tsokar cikin miyar. Amrah ta ce ba za ta ci komai ba wanda Fahimah ta dafa don bata marmarin tuwo, sai spicy chicken take so, ta kira Uwais tace idan ya dawo aiki ya tsaya ya taho mata da ita daga Chicken Republic. Amma Fahimah ba ta kyale ta haka ba, sai da ta yi mata dan wake da manja da yaji, ai kuwa Amrah ta yi ta zuqulqula tana shi wa Fahimah albarka. Ita kuma ta zage ta gyare gidan ciki da bai dinsa, dakin Uwais ne kawai ba ta shiga ba. Da ya dawo ya kawo wa Amrah kazar. Kallo daya ta yi mata ta ji ta ginshe ta. Ta ce, “Habiby, na ci dan waken Fah-himah na koshi kuma ku nemi mai cin wannanâ€?. Kwanan Fahimah bakwai a gidan gaba daya rayuwar gidan ta yi armashi. Amrah na samun hutu yadda ya kamata Fahimah na kula da cinta da shanta, tsaftar gidanta har ma da walwalarta. Wani irin sabo wanda ya fi kama da na ‘yan uwantaka ya shiga tsakaninsu. Uwais ya gaya mata Ammi ke rikonta ba ‘yar aiki ba ce kamar yadda ya gaya mata a baya, amma ko da wasa bai fada mata Fahimah daga orphanage ta zo hannun Ammi ba. A ganinsa wannan sirrin Fahimah ne wanda daga shi sai Ammi yakamata su sani, don sama wa Fahimah cikakkiyar walwala da sukuni a cikin mutane ‘yan uwanta. Uwais ya yi juriya kwarai, don kuwa bai kara attempting zuwa dakin Fahimah cikin dare ba, ya yarda da hujjarta na ce wa Amrah deserves respect, a gaban idonta ko a bayan idonta sabida kyakkyawar zuciyarta da kyautatawar ta.. Sati biyu na cika Fahimah ta soma shirya kayanta don komawa gida, Ammi ta yi waya gobe insha Allah za ta sauka a Kano. Amrah har da hawayenta da Fahimah za ta tafi, ta hada mata cosmetics designer din AVON set guda. Ita da Uwais da Fahiman suka tafi filin jirgi dauko Ammi. Suna ta hira ita da Amrah, Amrah na fadi mata “I cant' express my kind gratitude, for your being with me, for your kind assistance Fahhimah, ina ma Ammi za ta bar min ke mu ci gaba da zaman mu tare?â€? Uwais ya yi murmushi yana tukin mota zuciyarsa ta masa dadi, ya juya ya ce da Amrah da ke gefensa, “Ita kuma ta yi ta zama kenan ba za ta je gidan nata mijin ba?â€? Amrah cikin zolaya ta ce, “Ai don ta ki ne, amma na ce mijin ma ta zo mu aura tareâ€?. Uwais daga jin haka bai iya kara cewa komai ba, ko kwakkwaran motsi bai kara ba, don mamakin Amrah ya gama kashe shi. To amma ya ya za ta ji idan ta ji cewa all these while Fahimah zaman matarsa ta ke yi kamar ta? He is just fooling her? Ko ya ce they are just fooling her? Daidai lokacin da suka shiga filin jirgin Malam Aminu Kano, tuni su Ammi sun sauka, a reception suka hango ta. Fahimah da gudu ta runtuma ta rungume Ammi. Yayin da Ammin ke fadin, “Autar Ammi, na yi kewarku. Da fatan na same ku lafiya?â€? Amrah ta iso tana yi wa Ammi barka da zuwa. Ammi ta kama hannunta tana tambayarta karfin jikinta. Daga nan suka karasa mota Uwais ya ja suka tafi, amma wannan karon Ammi ce a gefensa, Amrah da Fahimah suna baya, hira suke sosai. Fahimah na ta bai wa Ammi labarai har suka zo gida. Baba Talatu ta yi musu girkin tarbar Ammi, Uwais da Amrah ba su jima ba suka wuce, Fahimah na kokarin kaucewa hada ido da Uwais a duk inda Amrah ta ke, haka yanzu da za su wuce ya biyo ta har dakinta yana so su yi sallama cikin gigicewa Fahimah ke korarsa. “Ka yi wa Allah Ya Uwais ka tafi, in yaso ka dawo daga baya, I cannot hurt this beautiful soul!". Gaba daya ta rude har tana tura shi waje da hannayenta. Shi abin ma dariya ya ba shi. Ya ce, “Zan tafi, amma ki sani kin ci bashi ba dan kadan ba, next haduwarmu biyan bashi ne, DEAL ne. Amrah kuma na gaji da wasa da hankalinta, don haka ki kwarara zuciyarki, soon ba da jimawa ba zan gaya mataâ€?. Fahimah ta ci gaba da tura shi, fatanta kawai ya fita a dakin. Uwais ya shammace ta ya hade bakunansu, kissing her deeply har sai da al’amura suka soma fin karfin Fahimah. Can cikin tsakar kanta ta jiyo Amrah na fadin. “Habiby, where are you?â€? Fahimah ta ja baya da karfi, trying hard ta yi pushing Uwais back, amma ta kasa. Wata irin kyakkyawar runguma ya yi mata yana fadin. “Fahhimah don Allah kada ki bar ni saboda Amrah, don na ga yanzu kin fi sonta a kainaâ€?. Fahimah ta gatsina baki, ta ce, “Da can din sonka nake yi Ya Uwais? Ka yi wa Allah ka tafiâ€?. Uwais ya ce, “Hummm! A bar kaza cikin gashinta, amma Fahimah na san kin dade kina son mara kirkin Yayan nan naki, dalili na na kara uzzura miki kenan, da kiranki da sunan da zai dinga bakanta zuciyarki don ki cire ni a ranki don na san duk ranar da Ammi ta gane hakan sunana angon Fahimah, ina so ko bana soâ€? To kana naka Allah na naSa, yau ga ni red - handed a dakin Fahhima cikin tafin hanun ta, ina begging for shan minti ana ture ni…â€?. Anyway bazan gaji da cewa ba kin burge ni, da ko Ammi bata taba sabin zuciyar ki ba. I salute your courage. Hannu ta sa ta toshe kunnuwanta tana fadin, “Yaya Uwais ka fita ko in yi magana da karfi Amrah ta san kana nanâ€?. “Da kin hutar da ni, don kullum shirya yadda zan fada mata nake yi kwarin gwiwar na subucewa, musamman da na gane tana son ki sosai". Daidai lokacin Amrah ta iso kwanar dakin Fahimah tana kiran sunansa. Juyawa ya yi ya fita, ya bar Fahimah tana sakin murmushi, in wani ya ce mata Uwais ne wannan din da gudu za ta karyata ba don ra’ayal aini abubuwan ke faruwa a gabanta ba. Lallai shi Allah mai canza al’amura ne zuwa duk yadda ya ga dama, kuma buwayi ne gagara misali, sannan ba abin da ya fi karfin ikonSa. Ta kwanta a hankali rigigine bisa gadonta tana tariyo dan abin da ya faru tana ta blushing ita kadai, amma wani bangare na zuciyarta ya shiga fargaba, fargabar ya ya al’amura za su kasance when Amrah comes to know the bitter truth din da ba ta sani ba??? ****** 9/23/21, 8:19 PM - Buhainat: Ta rasa irin godiyar da za ta yi wa Ubangiji da ya mallaka mata soyayyar Uwais. Amma duk lokacin da Amrah ta fado mata a rai sai ta ji gabanta ya fadi. Ya Uwais ya yi babban kuskure da su duka ba ta san ya za su yi da consequence dinsa ba. Ammi da ma ta ce babu ruwanta, shi da ya boye shi zai warware, wanda ya ja ruwa shi ruwa kan doka. Ita ba a boye ta yi hukuncinta ba. A yanzu kam babu tsanar Amrah a ranta don ta yaba da halayenta. Ko mata hudu Uwais zai kara aure a cewarta ba ta da matsala da su, tunda Fahimah ce uwargida, karatun Amrah a wata kasa shi kadai yake ci mata rai. A karshe kuma ta gode wa karatun na Amrah, don da ba don shi ba ba ta san ranar da Allah zai karkato da hankalin Uwais ga Fahimah ba. ****** Uwais ya sauka a kasar Switzerland lafiya, aka dauke su zuwa masaukin da aka tanadar musu. Thing are perfect ga hutu ga jin dadi, amma rashin iyalinsa ya sa ba ya jin dadin komai. Ita da ma Amrah ya daina sa ta a lissafi don ta gaya masa ya daina takura mata da kiran waya, da jidalallen cikinsa za ta ji mai tsirfar tsiya, ko da karatun da ke gabanta? A lokacin da ta gaya masa hakan, ransa ya yi matukar baci, ba ta ma tsaya ba ta saurari abin da ya kira ta ya fada mata ba ta fadi hakan, dama ya kira ta su yi sallama ne a kan tafiyarsa Switzerland. Don haka sai kawai ya sauke wayar daga kunnensa ba tare da ya ce da ita komai ba. Yasa a ransa ba zai kara kiran ta ba har ya bar kasar Switzerland. Kwanaki uku da yin hakan ta kira shi at her leisure time, shi kuma ya ki ya dauka. Sai ta turo text na ban hakuri da kalaman soyayya, ko kula ta bai yi ba, hankalinsa kacokam ya koma kan wadda ta ke da lokacinsa, wadda ita ko karatun ta ke yi ya kira ta za ta tsaya ta saurare shi, ita a kan karan kanta Fahimah tana kiransa idan kewarshi ta dame ta, wani abu da Amrah bata iya ba. Fahimah ta kan kira shi a lokacin da ta tabbata ya bar ofishin su na World bank zuwa masaukinsa. A wannan dan tsukin Uwais ya tantance da abu guda, gara ka auri matar da ke matukar sonka, a kan ka auri wadda ka ke matukar so. Domin ita wadda ka ke matukar so, in ta gane za ta yi ta wahalar da kai ne. Ita kuwa wadda ke matukar son ka, ko da daga baya ka zo ka kaunace ta da dukkan zuciyarka, ita a wurinta ka yi mata favour din ta ke kallonta as fortune. Probably zata yi hakuri da kai akan komai cikin kowanne hali. A typical example of Fahimah a gare shi. Sannan duk abin da yake hangowa a Amrah, sai daga baya ya samu kyal-kyal banza ne, farar fata kam akwai ta da dogon gashi, sannan ‘yar babban gida ce, ‘yar manyan 'yan bokon kasa. Amma a mua'amala ta auratayya ya fi samun nutsuwa da satisfaction daga mara kyale-kyalen 'yar marainiya wato Fah-himah. Su ‘ya’yan manyan mutanen sai mulki da iko da kansu. Ba kuma yadda za a yi da su. Cikin biyu ne ko daya; ko ka yi hakuri da su as they are ka nema wa kanka wata madafar, ko ka hakura da aurensu ba su da damuwa, domin suna hango wanda ya fi ka a komai. They may find thousands of you.... Wannan ya taimaka gaya wajen dusasar da tauraruwar Amrah daga zuciyar Uwais, ya dai saka a ransa ko me za ta yi masa ba zai sake ta ba. Don kuwa yana sonta har gobe. Amma zuciyarshi na kuna in ya tuna boko ya fi shi muhimmanci a wurin Amrah kuma za ta iya zabar karatun ta a kan aurensa. ***** Fahimah, ta ci gaba da zuwa makaranta don bayan sun gama exams ba su samu hutu ba zarcewa suka yi da sabon zango. Tafiyar Uwais ta samar mata da nutsuwa domin a da kullum cikin damuwa ta ke da takunkumin Ammi a kansa duk da bata nunawa, wanda ya maida shi Uwais dinsa na baya mara walwala, mara kula kowa. Zuwan Fahimah cikin rayuwarsa ya canza da yawa daga cikin odd behaviours dinsa, ya fara zama jovial har kafin Ammi ta sanya masa get da kebewa da Fahimah. Ammi da kanta ta fahimci walwalar da Uwais ya shiga a baya na da nasaba da samun hadin kan Fahimah da ya yi a Sudan, sannan walwalar ta ragu, da ta ce sai ya gama gini, ya kuma gaya wa Amrah gaskiya, sannan zai sake mallakar Fahimah a matsayin matarsa. Ba ta regretting decision dinta, domin ta ga yadda Uwais ya maida hankali a kan gininsa da kuma irin kudin da yake kashe wa ginin ya tabbatar mata Fahimah ta samu kyakkyawan matsugunni a zuciyar Uwais. Fahimah Shagari, dalibar tsimi da tanadi, ga ta da uwa farfesar tsumi da tanadi, idan suka dawo gida babu abin da Ammi ke yi sai koya wa Fahimah economics, assignment, test da statistics duka Fahimah ba ta da matsalarsu. Da aka yi jarrabawar zango na farko Fahimah 4.50 ta fito da shi. A hakan ma sai da Associate Prof. Safeeyyah Shagari ta yi wa Fahimah korafi cewa tunanin Uwais ta ke, shi ya sa aka kada ita maki 50 daga cikin CGPA din ta, bata tunanin cewa shi yana can yana kara gina kansa? Zata zauna ta maida kanta baya a kansa..... Fahimah sai ta yi murmushi kawai, don ita wannan makin ma da ta samu bata zaci za ta same shi ba. Da gaskiyar Ammi duk abinda ta fada ahaka yake. A kullum sallamarsu da Uwais ta ke tunawa which was so emotional; ya nuna mata kauna da soyayya mai tsayawa a zuci, mai kassara diya mace, wadda ta bar ta emotionally disturbed. A haka watanni uku ke gangara musu da ci gaba da nasara a tare da kowannensu. Dukkansu are goal oriented musamman Amrah is very determined. Wannan ya sa ta manta da mijin gabadaya, in har ba ta kalli zungureren cikinta bama ba ta tuno shi, shi ma ya yi banza da ita, don duk wata kulawa da yake so yana samu daga Fahimah cikin dare ta waya. Maganganun da Uwais ke wa Fahimah a waya na sanya ta a wani hali na tsananin kewarsa, ta ji ba abin da ta ke so irin ta bude ido ta ganshi tare da ita. Amrah ta shiga edd dinta ana saura sati biyu Uwais ya dawo daga Switzerland, kuma an yi sa’a lokacin suna gab da zana jarrabawa, don haka iyayenta cike da bacin rai suka ce ta taho Abuja, wata shekarar sai ta zana din. Ko kadan ba sa murna da wannan haihuwa ta Amrah ba ta cimma komai a rayuwa ba (a cewar Aunty Wasila). “Ke dabbar ina ce ki ka yarda ki ka dau ciki a wannan lokacin kamar wadda ba ta je makaranta ba? Ba ki san dan contraception na zamani ba? Ai shi ke nan sai ki yi deferring karatun ki zauna kula da jaririn Uwais, ba ki ganki ba duk kin bi kin tsofe daga aure shekara dayaâ€?. In ji Aunty Wasila ranar da Amrah ta sauka a gidansu da ke Apo. “Hasbunallahu wa ni’imal wakilâ€?. In ji Jabeer da ke shigowa, “Wasila, kina tsoron Allah kuwa? Kina son gamawa da duniya lafiya? Sunnar Annabin ki ke wa wadannan munanan maganganun haka? Ni dai wallahi Daddy ya cuce ku, kwata-kwata hanyar da ya nuna muku ta saba wa addini, da ba a yi auren ba a haife ku? Ko da an haifeku ba aure zaku so hakan? Zina ta yi ta samu cikin ko kuwa da kike mata wannan titsiyen? To ahir dinki a kan dan Uwais, don wallahi a kan wannan cikin daga ke har Amran zai iya daure ku har sai igiya ta yi rara!". Wasila ta zumbura baki daidai lokacin da Mamansu ta shigo. Ta ce, “Amrah me ki ke so a dafa miki?â€? Amrah wadda idonta ya cika da hawaye ta ce, “Mama ki yi min tsakani da Aunty Wasila, cewa nake ita ‘ya’ya uku gare ta? Ina ruwanta da cikina da za ta ce min dabba a kansa? Aure fa nake yi ba zina ba, ban ga dalilin da za a ce za'a bani query don an ganni da ciki baâ€?. Mama ta kyabe baki, ta ce, “masu aure manya, ke ki ka ga za ki iya, da ma Daddy ya ce yaron nan ya gama da ke, in ba a yi wasa ba karatun likita sai dai a ga kannenki da shi ban da keâ€?. Amrah ta fashe da kuka, ta ce, ta fasa haihuwa a gidan kada ta haihu su bi dare su kashe mata da, ta fuskanci duk ba sa son Uwais ita kuma tana son kayanta. Mama ta ce, “Ki fi ruwa tafiya, muna nan za ki dawo mana in dai namiji ne. Namijin ma irin wannan kallelen mai idanu a tsakar ka, daga ganinshi womaniser neâ€?...â€?. Amrah hannu ta sa ta toshe kunnuwanta, ta rasa me Uwais ya yi musu haka, daga Yaya Jabeer sai Aunty Murjanatu ke kaunar aurenta, amma a ce har uwar da ta haife ka?! Womaniser! Kalmar tayi tsauri da yawa a alaqantata da mutum mai daraja da mutumci irin Uwaiss. Wannan bakin cikin ya sa washegari ta tattara kayanta sai Kano. Ga shi tana cikin EDD bai kamata ta yi doguwar tafiya ba, amma da ta haihu a gidansu ta gwammace ta haihu a hanya, babu mai taba mata Uwais ta kyale. Ko da Daddy ya dawo Mama ta gaya masa Amrah ta yi fushi ta tafi, ta fasa haihuwa a gabansu don kawai Wasila ta gaya mata gaskiya, ta kwashe duk yadda aka yi ta gaya masa. Daddy a take ya dau waya ya kira Amrah, lokacin suna gab da shiga Kano ita da direban gidan su. Ya ce, “Amrah?â€? Ta ce, “Na’am Daddyâ€?. Ya ce, “kada ki sake in kara ganin kafarki a gidana, in kin haihu kuma babu wanda zai zo ki je ga ki dangin miji su yi miki komai da uwarki zata yi miki, ga da namiji nan don soyayya ku wuce Indiaâ€?. Amrah ta bude baki za ta yi bayani, Daddy ya ce, “Bana son jin komai, tunda duk abin da muke hango miki ba kya hangowa, we’re talking of your future which is ruined now…â€?. Kuka Amrah ta fara tana ba shi hakuri da kyar ya hakura, amma ya ce ba za ta haihu masa a gida ba. Amrah ta ce, “Na ji na yarda, amma don Allah ka yi hakuriâ€?. Ya kashe wayar ya rabu da ita. Jiki a sanyaye ta isa Kano, sai ta rasa ina za ta dosa, ba ta iya zama gidan ba Uwais, don haka ta ce da direba ya wuce da ita ‘Yankaba. Ammi da Fahimah na zaune suna karatu a falo, assignment na Fahimah suke solving. Ammi na nuna mata. Sai sallamar Amrah suka ji ta shigo tinkis-tinkis da tirtsetsen cikinta. Gaba daya suka hada baki wajen cewa, “Maraba da mutanen Malaysiaâ€?. Talatu ta shigo da jakar kayanta, wadda Maigadi ya shigo da ita. Fahimah ta karba sai ta wuce da ita nata dakin. Ammi babu sakewa sosai tsakaninta da Amrah don haka gaisawa kawai suka yi, da tambayar bayan rabo. Fahimah kuwa tuni ta tafi kitchen don hado mata abinci da abin sha. Har dare Amrah na zuba idon ganin ta inda Uwais zai bullo su wuce gida, amma shiru ka ke ji har karfe goma. Fahimah sai hidima ta ke da ita, dauko wannan miko wannan, da ta ga ta fara hamma daga zaune ta ce, “Aunty Amrah ko za ki shiga daga ciki ki kwanta?â€? Ganin idon Ammi ya sa Amrah ba ta furta damuwarta ta rashin ganin Uwais ba, ta bi shawarar Fahimah, domin sosai take son kwanciyar, suka yi sai da safe da Ammi, sannan ta bi bayan Fahimah zuwa dakinta. Fahimah tuni ta gyara mata gadonta, ta ce ta kwanta a gadon don ta fi jin dadi ita a kan lallausar bargo da ta shimfida a kasa za ta kwana. A lokacin ne Amrah ta tambaye ta ko Uwais sai karfe nawa yake shigowa? Fahimah ta juyo tana kallonta da mamaki, ta kasa cewa komai. Ita ce za ta gaya mata mijinta bai kasar? Abu wajen watanni biyu? To ba sa waya ne? A karshe ta ce, “Na ji Ammi ta ce, yana Switzerlandâ€?. Amrah ta zaro ido cikin kidima, Fahimah ba ta bi ta kanta ba ta ci gaba da shirin kwanciyarta. Wajen sha biyun dare Amrah tana barci wayar Uwais ta shigo wayar Fahima, kuma wayar tana kan bedside daidai inda kan Amrah ke kwance. Hasken wayar ne ya dame ta ta dauka don ta mika wa Fahimah don da alama ta yi barci, amma hoton da ya fito kan fuskar wayar ya sa ta mamaki hadi da bayyanar lambobin da daga gani ka san na kasar Switzerland ne. Abu biyu ya sa Amrah jin gara kawai ta amsa wayar nan. Don hankalinta ya kasa tsayawa waje guda. Dalilin Fahimah na dora hoton Uwais a kan lambarsa, da irin tune din da kiran ke bayarwa, sannan uwa-uba wane Yaya ne zai kira ‘yar uwarsa late at night haka? Lokaci ne na masoya da ma'aurata bana ‘yan uwa ba. Kawai sai ta amsa wayar ba tare da ta ce komai ba. She just want to confirm it's Uwais ko ta samu nutsuwa. Muryar Uwais tar-tar cikin yanayin da ke nuna akwai marital intimacy (sexual bond) ya ce, “Fahhima na kasa barci, wallahi hakuri na ya kare. Jiya saura kadan in maimaita irin laifina na Sudan, na ji tsoron Allah na ji tsoron fushin ki, musamman da na tuna tsiwar da ki ka yi min a ranar da tsanar dana gani cikin kwayar idon ki, na ce gara in rufawa kaina asiri in kashe ko nawa ne in miki ticket da visa ki zo min ko na kwana uku ne don Allah Fah-himah kada ki ce min a'ah, I’m missing everything, the luscious and succulent lips, your sweet...â€? kalmar karshe da ya fadi ya sa Amrah gigicewa don ko ni ban iya rubutata, wani karfin gwiwa ya zo mata. A nitse ta ce, “Ba FAHHIMAH ba ce, AMRAH ce…â€?. Sannan ta kashe wayar silently. Ta koma ta jingina bayanta a jikin gadon. Abin da ta kasa tantancewa shi ne, da ma tuntuni zaman miji da mata suke yi, ko kuwa farkarsa ce tuntuni suke blackmailing dinta? Ko kuwa Uwais extra-marital affair yake having da ‘yar rikon gidansu??? Ko da ta ce Fahimah ta auri Uwais, wallahi duk cikin lalurar yaron ciki ne, saboda a lokacin burinta kawai Uwais ya daina kusantarta, don ta daina jin qamshin (Maison Francis). Amma daga baya bayan ta samu ingantacciyar lafiya komawa ta yi tana cewa, “Allah ya sa ban fada da bakin mala’iku baâ€?. “Ni Amrah....Amrah Umar Dikko, ni Uwais ya yi wa haka???â€? Hawaye suka soma sintiri a kan fuskarta kafin wani azababben ciwon mara ya zo ya turnike ta. Salati ta shiga yi tana juyi don ba ta san nakuda ba, amma wannan ciwon da ta ke ji yau ta tabbata nakuda ce, amma da ta haihu a hannun farkar mijinta gara ta koma Abuja ko da da rarrafe ne......... 9/23/21, 8:19 PM - Buhainat: Washegari Amrah ta wuce Malaysia, da ma sati biyu za ta yi. Satin biyu ma cikin lokacin karatunta ne, ta yanke komai ne don ta samu ta gyara tsakaninta da Uwais, kuma ta samu ta gyara dan kadan ko ba duka ba duk da bai samu wata kulawa a tare da ita ba saboda lalura iri-iri na cikinta. A daren ranar bayan tashin Amrah daga airport gidan Ammi ya taho. Ammi da Fahimah suna zaune a falo suna kallon shirin Arewa24 Uwais ya yi sallama, hannayensa duka biyun zube cikin aljihu. Idanunsa straight a saitin Fahimah wadda daga amsa sallamarshi ta mike. Ta ba su wuri shi da Amminsa. Ba ta yarda ta kalli Uwais cikin ido ba sabida Ammi, kuma dai ba ta hango komai a tare da shi sai tsagwaron rigima yau, tunda ya koma gwauronsa kamar da. Ammi ta amsa mishi, ya zauna suna kara gaisawa, ta ce, “Yan Malaysia an tashi kenan?â€? Ya ce, “Eh Ammi ta tashi yanzuâ€?. Sannan ya sunkuyar da kai cikin jin nauyin abin da zai fada. “Ammi na zo ne tafiya da Fahhima, sai ta zauna gidan Amrah kafin a karasa nata ginin. Ammi kin ce duk ranar da na shirya karbar aurena da Fahimah da hannu bibbiyu ranar ne za ki ba ni ita. Yau ga ni da kokon barana Ammi, gwiwa a kasa, ki yi min alfarma ki ba ni Fah-himahâ€?. Haj. Safeeyah ta gyara zamanta tana kallonshi sosai, kamar mai son hango reality na maganganunsa cikin kwarar idanunsa. Daga bisani ta ce, “Uwais, ka gaya wa matarka cewa kana auren Fahimah?â€? Ya girgiza kai, ya ce, “A’ah tukunna Ammi, sabida na ga tana gidan, kuma Amrah ba ta gama samun karfin jikinta baâ€?. Ammi ta yi wani miskilin murmushi, ta ce, “To ba da ni za a yi aikin rashin gaskiya ba, kuma Fahimah ba za ta je gidan matarka da kayanta a ciki da iyayenta suka zuba mata ta yi zaman aure ba. Har sai ranar da ka zaunar da ita ka gaya mata cewa tare aka daura aurenta da na Fahimah, sannan ka kammala wa Fahimah ginin gidanta ita kadai, don ba za su zauna tare ba. Sannan zan yarda ta tare. Duk wannan ‘yar dadin da ka ga suna yi, ina tabbatar maka don Amrah ba ta sani ba ne, da tuni komai ya rushe. Don haka ka je ka gama da wadannan matsalolin na gabanka kafin ka zo gabana da neman daukar matarka. Sannan Uwais, na hana ka shiga dakin Fahimah daga rana irin ta yau, daga lokaci irin na yau, sai kun koma gidanku, don ni ba tsohuwar banza ba ce, da za ka dinga binta daki a gabanaâ€?. "Yau dai Ammi tsagwaron mugunta ta ke ji!â€?. Uwais ya fada a ransa, gumi na karyo masa ta kowacce kafa mai fitar da gumi a jikin dan adam. Gini kam ya yi nisa amma bai karasa ba ai. Amrah kuma in ba ta waya ake so ya gaya mata ba, cikinsa ya zube bai san ta hanyar da Ammi ke so ya je ya gaya matan ba. Ya shirya a ransa ne sai ta dawo wannan hutun, nan da watanni hudu, lokacin cikinta ya kusa isa haihuwa. Ya share gumin da ke faman tsatstsafo masa a goshi. Da dai Ammi zata bari sai gobe ta sa masa wannan takunkumin. Yau ta barshi yayi sallama da matar sa. Yau sati biyu kenan rabon shi da Fahhimah.....Fahhimar da ta zo ta canza akalar rayuwar shi gabadaya ta juya ragamar ta cikin dan lokaci kalilan, gaskiyar magana a yanzu bai iya rayuwa ba tare da ita ba!!! “Ammi, duk abin da ki ka lissafa zan yi. Amma ki yi hakuri sai Amrah ta dawo hutu. Yanzu zan maida hankali a kan ginin, ki taya ni addu’a Allah ya hore in gama shi cikin dan lokaciâ€?. Yana gama fadin haka ya mike zai fice ko ganin gabansa ba ya yi, imagining yadda zai karar da daren yau babu Fahhimah, bayan har Allah-Allah yake Amrah ta koma ya samu wannan damar, don kuwa ba ta amfana masa komai tun zuwanta sai tsurfa da korafi irin na masu juna biyu. Na Amrah har da karin sangarta a ganinsa, kamar a kanta aka soma ciki. Allah kadai ya san iya burin da ya ciwa daren yau. Don haka washegari ya bude wuta a kan ginin Fahimah kamar zai shiga ayi da shi, wanda ake yi a Unguwar Sulaiman Crescent. Ya bai wa ma’aikatan watanni biyu su kammala komai. Komai da ke account dinsa ya tafi ya shige cikin aikin ginin don so yake a yi mata komai kamar na Amrah. Ammi zuciyarta kal! Ganin yadda Uwais ya gigice da hukuncin ta. Burinta ta saya wa Fahimah martaba kamar kowacce mace a gidan miji, in ta ci gaba da barinsa yana zuwa yana rage dare ba zai maida hankali ga muhimman al’amuran ba, gini da sanar da matarsa gaskiyar magana. Ita ba girmanta bane wannan boye-boyen da yake wa Amrah. Gara ayi ta ta kare. ***** Fahimah ta ci gaba da zuwa makaranta tare da Ammi, Uwais sabida haushin Ammi ta ce ba zai kara kebewa da Fahimah ba yanzu sai ya yi kwanaki uku bai zo gidan ba. In ya zo kuma ba ya zama, abinci kawai yake ci ya tafi, in Fahimah na zaune a falon su gaisa yana faman kawar da kai, in ba ta falon ba ya nemanta. Hakan ya fi komai sauki ga Fahimah don karatunsu ya fara zafi, sai ta maida hankali ga karatu sosai, da tukin mota da Ammi ke koya mata da yamma don ta ce ta fasa na Uwais din, don zai iya amfani da damar ya karya umarninta. Don haka ta zage tana koya wa Fahimah tukin da kanta at her leisure time. Allah cikin ikonsa kuma da yake ya sa pressure sosai cikin watanni biyu ginin gidan Fahimah ya kammala, har fenti da komai an gama. A ranar da yake shirin gaya wa Ammi, ya samu takarda daga babban bankinsu na kasancewarsa cikin wadanda banki ya zaba ya tura kasar Switzerland yin wani muhimmin course da World Bank. Abun farin ciki ne a gare shi domin in ya dawo karin matsayi zai samu, amma da ya tuna tafiyar na nufin nesanta shi da Fahimar da yake ganin ya kusa samu, sai duk murnar sa ta koma ciki. Yaji kadaicin duniya da damuwar duniya sun lullubeshi kamar shikadai ya saura a fadin duniya. Na farko dai ba a ba su damar daukar iyali ba, na biyu ko an ba su Fahimah ba za ta samu binsa ba domin tana gab da zana jarrabawarta ta karshen zango. Kwas din na watanni uku ne, kuma su goma kadai suka samu wannan babbar alfarmar. Za su tashi da zarar visa dinsu ta kammala. A ranar ya zo ya gaya wa Ammi, maimakon ta ga yana murna ta fahimci jikinsa a sanyaye yake. Kuma cikin matukar damuwa yake. Ammi is over-excited domin da ma akwai kyakkyawan shiri da ta ke son yi wa Fahimah wanda a baya ba ta yi mata sosai ba. Gara-gara ma a Sudan ta dan karba ta bata a wajen matar Mahdi. Tafiyarshi zai ba ta damar yin komai a nitse, in ya so da ya dawo sai su koma gidansu. Ammi ta ce, “Wannan ai abun farin ciki ne Uwais, tunda ci gaba ne ta fannin aiki. Allah ya tsare Ya bada nasara. Ita ma Fahimah jarabawa za ta yi, don haka in ka dawo sai ku wuce gidan ku insha Allahâ€?. Sallamar Fahimah da Uwais ta kasance a wani dare na litinin, bayan ya dawo aiki ya zarto gidan, ana i-gobe zai tashi zuwa kasar Switzerland. A kalla ya shafe kwanaki masu yawa bai sanya Fahimah a idanunsa ba, kuma bai neme ta ba, don Ammi gasa shi ta ke ba da wasa ba. In taga lokacin zuwansa ya kusa sai ta tashi Fahimah daga falon ta sata wani aikin. Ita kuma ta kasa ta tsare a falon taki zuwa ko nan da can. Sun yi sallama da Ammi har zai wuce ba tare da ya tambaye ta Fahimah ba. Ransa a cumkushe. A zuciyarsa yana fadin, “Ammi ga ‘yarki nan gabadaya na bar miki har wata uku, sai ki yi ta kullewa a daki. Tunda dai duk kawaici na ba a gani baâ€?. Shi kadai ya san halin da yake kasancewa a ciki duk daren Allah a gidansa ba Amrah ba Fahhimah, kuma ya yanke shawarar kin kiran Fahimah a waya har sai ranar da suka gama masa gashin kumar ita da Ammin ta, don ita ma ta biye wa Ammi ba ta nemansa, ta durfafi karatun makarantar ta, ba ji ba gani. Amrah ko ko ya kira ta ma yanzu ba ta iya doguwar hira barci zai yi awon gaba da ita. Ko ta ce masa ita karatu ta ke yi ya bari gobe za ta kira shi, sanda ta ke free din, shi kuma yana ofis yana fama da ayyukansa. Don haka in ka ga Uwais a dan tsukin nan har ramewa ya yi, ya fada sosai, ga kasumba ta taru ya ki ya aske ta. Sosai yake ragaita a zuci da gangar jiki. Bayan sun yi sallama da Ammi zai wuce, sai cewa ta yi. “Ba za ka shiga ku yi sallama da Fahimah ba?â€? Idanun Uwais suka kifta kadan, ta wani fannin tamkar wanda aka aikowa da manzon Rahma, wani kuzari ya da rabon sa da irin shi tun ranar da ya zo daukar Fahimah su tare a gidan sa amma ta gwale shi da takunkumin ta, ya ce, “Ammi kin yi izni?â€? Da murmushi a bakin Ammi ta ce, “Na yi izni Uwais, ko da ma can ai ban hana ku gaisawa ba a waya ko a falon nan. Na fi so ne dai ta tare a dakinta, sannan ku je ku karata. Amma sallama ai ta zama doleâ€?. Tana gama fadin haka ta wuce zuwa dakinta, ta ce da Uwais, “Saduwar alkhiriâ€?. Ammi na bada baya Uwais ya juya dakin Fahimah da takunsa na sassarfa. Tana kwance tsakiyar gadonta ta rufe kanta da pillow, amma ba barci ta ke ba, tunanin Uwais ta ke yi da tsawon lokacin da suka dauka ba tare da juna ba alhalin suna gida daya, kuma suna jin muryar juna sau tari cikin gidan, sannan su kan ga juna jefi-jefi. Ba ta san dalilin Ammi na nesanta su da juna har haka ba, amma ta yarda komai Ammi za ta yi akan su, to za ta yi ne for her own betterment. Itama ta fi yarda Amrah ta san me suke ciki in ya so komai ta fanjama-fanjam, kuma tana bayan Ammi na ba za ta shigar wa Amrah gida ba don ba ta nan. Da murda kofarsa da sallamarsa ciki-ciki duka ba ta ji su ba. Sai kwanciyarsa a gadon bayanta. Ya sakar mata dukkan nauyin sa. An ce duk nauyin miji mace na dauke shi tsaf ba tare da ta ji nauyin ba ita. Amma Fahimah har ‘yar kara ta saki sabida nauyin Uwais. Dadi da cewa ba ta tsammaci zuwansa a lokacin ba don ba ta san da tafiyar da ke gabansa ba. Daga haka Uwais ya canza akalar komai zuwa irin wadda ya fi so a rayuwarsa (romansiyya), wato kasancewa tare da Fahimah cikin nau’ikan soyayya irin nasa mai keta zuciya da ruhin Fahimah. Al’amuran da suka biyo baya masu tsauri ne kwarai a tarihin rayuwar auren su. Sai da dukkansu suka samu nutsuwar da suke bukata, Uwais ya maida sittirunsa ya rike Fahimah cikin hannayensa, fuskarta cikin tafukansa. “I’m going to Geneva Fah-himah, sai bayan watanni uku zan dawo. It will not be easy kin sani. Amma as a man dole in je in nemo muku abinci. Ki kula min da kanki. I will surely miss you and everything of you... this luscious lipsâ€? I’m gonna miss themâ€?. Fahimah ta janye fuskarta daga tafukansa cikin tsananin damuwa, sannan ta kwantar da kai a kafadunsa sai ga hawaye suna zuba tarara! Wata uku! Babu Uwais! Na nufin komai a gare ta...., Uwais ya sanya dan yatsar sa ya lakato hawayen ya ce, “Better, bayan muna gari daya ma kin biye wa Ammi kun sanya ni a kwandon shara, shi ne yanzu ki ke wani kuka, how dare you want me to believe you cewa hawayen a kan tafiyata ne???â€? Fahimah ta ce, “Yaya Uwais ba za ka gane ba. I love you so muchâ€?!â€? Ta sake kankame shi tana kuka. Amrah ta sha gaya masa wannan kalmar, amma yau da Fahimah ta fada wani madaukakin farin ciki ne ya lullube shi, wani excitement ya bakunce shi, ya yi mata kyakkyawan muhalli a cikin physique kirjinsa yana shafa kwantaccen gashin kanta. Sun dauki lokaci mai tsawo a haka kafin Uwais ya dago fuskar Fahimah cikin tafukansa, ya soma magana cikin taushin murya. “I’m sorry for all the past inconveniences, I’m sorry for the rest of our lives. Fahhimah I hurt you so much cikin ajizanci irin na dan Adam. Da Ubangiji ya tashi hukunta ni sai ya hukunta ni ta hanyar sanya min sonki da kaunarki lokaci daya. Ba tareda na shiryawa hakan ba. Today .... i must confess......ban sani ba ko in na tafi bazan dawo ba, I want to use this medium to tell you aloud that I LOVE YOU very-very muchâ€?!!!â€? Suman wucin gadi Fahimah ta yi a tsaye, Allah ya so ta jikin Uwais ya yi mata garkuwa, ba don haka ba sulalewa za ta yi a kasa ta narke domin farin cikin is over-estimated. Cikin yanayin da Uwais da Fahimah suka kasance kenan na lokaci mai tsawo ba tare da sun ankara da tafiyar lokaci ba, sai kiran assalatu suka ji a tsakar kansu. Dole tare suka yi sallar asuba bayan sun yi wanka. Sannan ne Uwais ya yi haramar tafiya amma ko ya tafi idan ya je bakin kofa sai ya dawo, kamar ba za su rabu ba, ganin watanni uku suke tamkar shekaru uku. Sai da alarm din gefen gadon Fahimah ya buga karfe bakwai na safe sannan Uwais ya iya tafiya. A wannan yanayi Fahimah ba ta yi barci ba, ta karar da ranar wajen addu’a ga Uwais da nema masa sa’a a wannan tafiya tashi da nema masa albarka a cikin nemansa. Ko da Uwais ya shiga jirgi kafin su tashi, sai da ya fara kiran Fahimah. Da ta dauka muryarta rawa ta ke da alama ta ci kuka ta koshi. “Yaya Uwais kun tashi?â€? Ya ce, “Are you crying Fahhimah? Me ya sa ki kuka?â€? Ta share hawayen ta ja hanci, sannan ta ce, “Gani nake kamar in ka tafi ba za ka dawo ba as you saidâ€?. Ya canza positon na rikon wayarsa, ya ce, “Fah-himah, in kin ga ban dawo gareki ba, to na mutu acan, wanda bana fatan hakan yanzu. I would like to cuddle your black beauty babies in my arms..…â€?. Wani hawayen ya zo wa Fahimah, amma this time around na farin ciki ne. “Yaya Uwais kana son ‘ya’yana? Idan suka yi baki kamar ni fa?â€? Uwais ya ji duk ya muzanta, nadama ta kara lullube shi, shi ya sa ba a son gorin halitta don ba ka san me gobe za ta haifar ba. Muryarshi ta yi rauni kwarai a sanda yake cewa, “Dan Adam ya kasance ajizi mai yawan kuskure, kuma Uwais yana cikin su. I’m sorry Fahima for the past weird experiences which are all regretful. Yau kin sa na yi nadama irin wadda ban taba yi ba. Fahimah ‘ya’yanki, jikokin Ammi ne, sabida ‘yar ta ce wadda haifa ne kawai ba ta yi ba ta haifo su, sannan sun fito daga jikin Uwaisâ€? with all these .... and much more....zan so su fiye da yadda nake son kaina!â€?. Hawayen Fahimah suka ninka na baya, farin cikin ya ninka na baya ta ce, “Ya Uwais na yafe maka, na kara yafe maka, ni da ma kullum uzuri nake yi maka. Is not easy da ma a so ‘ya’ya kamana sai ga exceptional mutane irin su Ammi, wadanda su kuma tsiraru ne a cikin al’ummah. Ban taba rike ka ba ko da sau daya a zuciyata sabida an ce so hana ganin laifi, and I blindly love you at the time, fatana kawai shi ne ni ma ka so ni ko da rabin-rabin yadda nake sonkaâ€?. “And you got it Fah-himah, halayenki sun sayo miki soyayya fiye da wadda ki ke kintace. Also bazan gaji da cewa ba you are a darling (ke abar so ce) da duk namijin da Allah ya yi wa baiwar samunta, hakika ya ba shi rabin addininsa. Ya yi masa boyayyen gata irin wanda kudinsa da zabensa ko mulkin sa bai isa ya ba shi ba. Ba ni da abin da zan ce wa Ammi a yanzu, sai dai in dauwama ina roka mata aljanna ita da mahaifinaâ€?. A lokacin aka soma shela cikin jirgi cewa a daura belt jirgi zai tashi hakanan. Haka Uwais ya yi sallama da Fahimah jiki a sanyaye don har zuwa lokacin Fahimah ba ta daina kuka ba. 9/23/21, 8:19 PM - Buhainat: Ta turo baki gaba, ta ce, “Kawai zan yi kewar Ammi neâ€?. Ya ce, “Uwais fah?â€? Ta kyabe baki, “Ko kadan ba zan yi baâ€?..â€? Dariya ya yi ya ce, “Ohk, Amrah, is waiting, I’m leaving now, amma ki sani kina gab da tarewa a gidan ki da zarar Ammi ta dawoâ€?. Ya mike bayan ya bata kyakkyawar sumba a goshi. “Kin ce ba za ki yi kewata ba, ni kuma I will undoubtedly miss EVERYTHING da ke faruwa ko ya faru tsakanin mu in these few days... in na ce komai ina nufin KOMAI.... especially our Dambe, our first night, our Lagos life, our Sudan life, and our past inconveniences. I will still NOT say I love you sai ranar da na samu kyakkyawar sumba daga gare ki, sai ranar da ki ka tare a dakin ki, ki ka karbi girkin ki. In hakan ta faru na fi kowa sa’ar zuwa duniya. I remain loyal to my mother, thankful and prayerful to her da ta mallaka min ke Fahhimah…â€? Fahimah ta runtse idonta, kalaman Uwais na ratsa ta, suna gasa kowacce gaba ta jikinta tamkar a cikin oven. Amma kunya ta sa ba ta ce masa komai ba. Ya sake sumbatar goshinta, sannan karan hancinta, ya ja tunga a lips dinta, ganin zai zarme ga wayar shi na ta tsuwwa alamun matar shi ta gaji da jira, sai ta janye kadan. “Please goâ€?..â€?. Ta fada cikin karfin hali irin nata. “Korata ki ke yi Fah-himah?â€? “Ba girkina ba ne, babu kyauâ€?. “Ai ba a raba girkin baâ€?. “Ni dai don Allah ka tafi Ya Uwaisâ€?. Ta fada da iyakacin courage din ta. Cikin shagwabar da ta kara tunzuro Uwais ya kasa tafiyar, sai kallonta cikin tsananin bege. Wayar shi ta kara daukar ringing da tune na musamman da ya sanya wa Amrah. Dole ya juya ya tafi a sanyaye, don Fahimah ta juya da sassarfa shige dakin ta. Tana shiga dakin ta rufe kofarta, ta jingina da jikin kofar tana maida ajiyar zuciya mai nauyi. Ta san barci yau zai yi wuya a gare ta, amma ta sa a ranta gara ma ta saba, Amrah ma na da hakki a kansa, kishi ba nata ba ne ita matar shige, don ta samu Allah ya kankaro mata 'yar darajar da mafarkin ta bai taba bata ba, bai kamata ta yi butulci ba. Amrah ta cika fam, ta yi fushin har ta gaji. Lokacin da Uwais ya iso gidan Murjanatu, suna gaisawa shi da Aunty Murja a falo. Aunty Murja ta ce ta dauko jakarta su tafi, sai kumburi ta ke haka ta dauko jakar ta bi bayansa. A cikin motar ya yi mata side hug sannan ya ba ta hakurin rashin zuwansa da wuri. Ta ce ita ba ta hakura ba, sai ya gaya mata inda ya je. Ya maida hankalinsa ga tukin motar, “Amrah ki yarda da ni ba inda na je, ina gidaâ€?. Ta san ba zai mata karya ba, don haka ta bar zancen. “Me za ki ci mu tsaya mu saya kafin mu karasa gida? Bana son sake fitowa in na shiga, don a gajiye nake". Amrah ta yamutse kyakkyawar fuskarta ta ce, “Ai ni yanzu ba komai nake iya ci ba Habiby, sai abu mai dan yaji-yaji, mu biya Chicken Republic ina son spicy chicken din suâ€?. Ya bi umarninta. Suna zuwa gida ta zuro kafar ta daya waje tana kokarin fitowa daga motar, sai ta juyo ta ce da shi, “To amma fa Habib Qalby, ba za mu hada daki ba, wallahi ko kadan yanzu bana son turaren kaâ€?. Cikin mamaki yake dubanta baki a sake. “Amrah lafiyarki kalau kuwa?â€? “Sumul kalau nakeâ€?. “To kam, ai sai dai in canza kayan, amma abin da ki ke fadi ke ma kin san ba mai yiyuwa ba neâ€?. Amrah kamar ta saka kuka, ta ce, “Wallahi ko ka cire ba ka daina kamshin (Maison Francis)â€?. Ya ce, “Ai kuwa sai dai a yi wacce za a yi, amma ban da wannan yarenâ€?. Sun yi shirin kwanciya, zullumi da damuwa duk sun ishi Amrah, ba da wasa ta ke ba turarensa hawa kanta yake, a baya babu kamshin da ta ke so irin na Uwais amma banda yanzu. Uwais na sanya tafukansa a bayan wuyanta ya hada goshinsu zai lallashe ta don ya ji actual abin da ke damunta ta ke ta wannan yamutse-yamutsen fuskar. Ai kuwa ta kelayo masa wani uban amai, mai karni. Ya yi maza ya ja baya ita kuma ta ci gaba da amayar da spicy chicken din da ta ci tas! Sai da ta amayar da ita. A daren ya ce su tafi asibiti, ita kuma ta dage ba ta zuwa ko’ina. Ai ta gaya masa turarensa ne ba ta so ya ki jin magana. Ya ki ya bar mata dakin. Washegari sai da ya yi mata jan ido sannan ta yarda suka tafi asibitin standard. Awo na fitsari a tashin farko ya nuna ciki na watanni uku. Tunda suka dauko hanyar dawowa Amrah ke kuka, kuka kashirban. Kamar ba ita bace a baya ta ce ta yi surrender ba. Bata taba tsammatarwa kanta ciki a wannan lokacin ba. Ta rantse ba ta shirya wa haihuwa yanzu ba, karatunta zai salwanta. Uwais sabida tsananin bacin rai ga kalaman Amrah a kan kyautar da Allah ya yi masa cewa ya yi, “Wallahi in ki ka zubda cikin nan da gangan, to a bakin aurenkiâ€?. Amrah ta zaro ido tana kallon Uwais, kallon mamaki da tsoro, ina soyayyar da yake ikirarin yana yi mata? Yanzu har ya fi son dan da zai haifa a kanta? Da ma Daddy ya ce soyayya karya ce, ka yi aure kawai don bukatarka ta dan Adam da cika sunnar Annabi, amma ba don soyayya ba, sabida it never exist in nowadays men, even if it exists da zarar sun gano wata za ta yi fading. Shin Daddy da gaske yake? Ko dai Uwais ya gano watan ne shi ya sa komai nata ke fading a idanunsa??? Ba za ta yi mamakin kowacce barazana daga gare shi ba, don ya nuna yana son cikinsa. Amma barazana da igiyar aurenta abin ya ba ta mamaki da tsoro sosai, ya kuma kara sagar mata da gwiwa akan canje-canjen data ta gani daga gare shi. Tunda suka dawo kuwa ta raba daki da shi, shi ma bai kara takura mata ba. Yanzu lallabawa zai yi ta haife masa dansa ko ‘yarsa lafiya ya daina neman komai a wurinta. All thanks to AMMI yana da precious gem dinsa a gefe, a virtous wife who her priçe is far above rubies wadda sai yadda ya ga damar sarrafa ta (naïve and innocent FAH-HIMAH SHAGARI). Yau da bai san ina zai sa kansa ba da wannan takunkumin na Amrah. Wuni guda Amrah ba ta kulla komai a gidan ba, ga shi duk ya yi kura, kasancewar an kwana biyu ba'a ciki, tunda suka zo sai abincin sayarwa yake ta faman sayo musu. Har ya fara gajiya da daukan mota yana fita yana dawowa. Ita da kanta dattin gidan ya ishe ta, ta fito ta same shi a falo yana kallon ball da kungiyar da yake so Arsenal, yana shan wankakken inabi da ke kan tebirin gabansa. Daga can nesa da shi ta tsaya tana toshe hanci. “Habiby, ina wannan yarinyar ta gidanku?â€? Ya kalle ta cikin takaicin yadda ta ke toshe masa hanci kamar wani mushe, ya ce, "Wace yarinya? Mu gidanmu da yarinya ne?â€? Ta ce, “Wannan budurwar nake nufi, baka, mai kyau haka, mai jan class din nanâ€?. Gaban Uwais ne ya bada wani irin damm! Ya bude ido kawai yana kallon ta. Ta ce, “Don Allah don Annabi ka je ka dauko min ita ta taimaka min in kintsa gidan nan, ta yi min miya ko ta sati daya ce in sa a firji don wallahi ba ni son warin albasaâ€?. Uwais ji ya yi tamkar Amrah ta yi masa gafara, zaman nan da ya yi yana shan inab tunaninta yake yi, ba ya son Amrah ta samu wani clue ne kasancewar Fahimah matar sa a yanzu, musamman cikin halin nan da ta ke ciki komai zai iya faruwa. Ya yi niyyar gaya mata gaskiya tun kafin ya baro gidan Ammi, amma sai ga bayyanar maganar cikin, don haka ya fasa sai cikinta ya yi kwari. Ta yadda ko me ye zai biyo baya ba zai shafi lafiyar babynsa ba. Amma anya Fahimah za ta yarda ta zo gidansa? Kuma in ya yi hakan ya yi wa Ammi da ita kanta Fahimar daidai duk da Amrah taimako ta nema? Amma Amrah ta kafa naci, ta kasa ta tsare ita lallai ya je ya zo mata da mai aikin Ammi. Da ya rasa yadda zai mata bayani, sai ya fiddo wayarsa ya binciko lambar Ammi ta kasar Sudan ya kira. Wayar na shiga ya mika mata, “Ungo nemi iznin Ammi da kankiâ€?. Tana karba ta yi sallama, “Salamu alaikum, Ammi ni ce Amrahâ€?. Ammi ta ce, “Maraba da mutanen Malaysia, ya ya karatun?â€? “Ammi na samu mid-term break na sati biyu shi ne kawai na taho Kano. Amma Ammi ba ni da lafiya, ba na iya aikin gida da girki, shi ne na roke shi ya dauko min aron yarinyar wajenki kafin ki dawo, lokacin ne nima zan koma makaranta, tunda ita ma cikin kadaici ta ke, sai mu zauna tare ta taimaka mun har ki dawo, sai ya ce wai sai dai in tambaye ki da kaina. Don Allah Ammi a yi min alfarmaâ€?. Ammi ta yi jimmmm! Kafin ta ce, “Babu laifi, zan masa magana ya dauko ta ya kawo miki, amma ku bari in fara magana da ita tukunna in nemi amincewar ta. Don Fahimah ba wai ta saba da shiga mutane ba neâ€?. Amrah ta ce, “Ki roka min ita Ammi, ki gaya mata I’m not boring, ba zan dinga damunta ba sam, hira in ba tana so ba ba za mu yi ba, ni ma ba dadi nake ji ba kullum ina daki, sabida warin komai sai in ji shi ba daidai ba…â€?. Ammi ta yi murmushi, ta ce, “A hankali komai zai dawo daidai, zan lallashi Fahimah ta zauna da ku din har in dawoâ€?. A zuciyarta kuma addu’a ta yi, Allah ya bai wa Fahimah nata rabon itama cikin gaggawa. Ta rasa dalilinsa na kin gaya wa Amrah gaskiya cewa Fahimah kishiyar ta ce, amma ta san Uwais sarai ta san halayensa, ko me yake yi yana sane, kuma sai ya tabbata yana da hujja. Kafin ta kira Fahimah sai da ta fara kiran Uwais a lokacin da ta tabbatar yana office. Ta ce, “Uwais me zai hana ka gaya mata gaskiya in ya so Fahimah ta tare gabadaya su yi zaman mai dalili? Ni bana son abu na rashin gaskiya ko kankani, kada nan gaba ta gane ta ce mun yaudare ta". Uwais ya ce, “Ammi ki rabu da Amrah kawai, zan gaya mata amma ba yanzu ba, don ba son cikin jikinta ta ke ba. Idan na gaya mata yanzu komai zai iya faruwa. Za ta iya yin komai don ta huce wanda zai kare ne a kan cikin nan, don hakan sai nan da watanni hudu a gaba zan gaya mata. Lokacin na gama yi wa Fahimah gininta. Ita kuma cikin ya kusa isa haihuwa. Don yanzu na aza harsashin gininâ€?. Ammi ta fahimce shi, as she has no option, ta ce, “To Allah ya kade fitina ya hada hankulansu in ka tashi sai ka biya ka tafi mata da Fahimar zan kira ta yanzu in mata bayani". Fahimah ta fito wanka kenan tana shafa a gaban mudubi kiran Ammi ya shigo mata. Ta mika hannu ta daga da sallama, Ammi ta ce, “Ya ya na ji muryarki so pale? Are you alright?â€? Fahimah ta ce, “Lafiya nake Ammi, barci ne bai ishe ni baâ€?. Ammi ta ce, “To ki kwanta zuwa lokacin tashin Uwais zai zo ku tafi gidansa. Amrah ta roke ni kan ba ta da lafiya ki je ku zauna tare kafin na dawo. Ki sa a ranki Amrah ba kishiya ba ce a gare ki, kanwa ce. Ko babu aure tsakaninki da Uwais in tana cikin lalura hakkinmu ne mu taimaka mata tunda iyayenta ba a gari suke baâ€?. Fahimah ta ji kanta ya yi wani irin gingiringim. Idan kuma Uwais ya bada wata kafa da Amrah za ta fahimci something in between a tsakaninsu fa? Tunda daga shi har Ammi ba su shirya bayyana matsayinta ga Amrah ba? A kan dalilinsu da ba za ta ce mene ne shi ba? Amma matsayin Ammi ya wuce ta yi umarni ta saba, ko da bai yi daidai da son ranta ba. Ammi ba ta yi haka don ta kaskantata ba, sai don ta zamo uwa mai adalci ga kowa (zuciyarta ta tunasar). Sai kawai ta mike ta hau shiri, tana addu’a a cikin ranta, Allah ya ba ta juriya a zama da Amrah da zata je ta yi, ya rage mata kishinta da ke damun ranta. Sanda Uwais ya shigo gidan a falo ya tadda ita jingine jikin jakar kayanta da ta hada. Ya tafi gaba-gadi da sassarfa ya yi mata wata kyakkyawar runguma tamkar ya tsaga kirjinsa ya sanya ta. Ya yi kewarta yadda harshensa ba zai iya bayyanawa ba. Sai ya shiga nuna mata practically yadda ya yi kewan nata har abin ya bai wa Fahimah mamaki da tsoro. Tsoron nata bai je ko’ina ba ta ji Uwais ya sure ta bai aje ta ko’ina ba sai tsakiyar gadon dakinsa. It was kind of gentle romance wanda ya motsa zuciya da ruhin Fahimah har sai da hawaye suka fito daga idanunta. Hawayen da ta tabbatar na farin ciki ne, farin cikin cikar buri, burin mallakar Uwais a rayuwarta, ta tabbata da ba ta samu Uwais ba rayuwarta ba za ta taba komawa cikakka, kuma mai dadi ba kamar yadda ta faro a baya. A bangaren Uwais 100% satisfaction irin wanda bai taba samu a rayuwarsa ba. Da komai ya lafa a tsakaninsu ya koma gefe tallafe da kansa yana kallon Fahimah daga karshen idanunsa yana mamaki yana tu’ajjibi a cikin ransa na yadda ta juya masa rayuwa cikin dan lokaci kalilan. Ya manta da asalin, ya manta da kalar fatar da ba ya son, ita din kadai yake son kasancewa da, fiye da kowa a halin yanzu. Ita ce sirrinsa marufar asirin sa. Inda yake jin zai iya sauke duk wani urge da bukatun sa babu shamaki. Hannu ya sa ya janyo ta gaba daya ta dawo samansa. Ya ce, “Fahhimah, yau hira za mu yi, madallah da Ammi na, uwata wadda ta fi ta kowa, da ta mallaka min this rare gem. Fahhimah ki ba ni labarin duk da ya shafe ki da na rayuwarki, ina kuma son sanin duk abin da ki ke so da wanda ba kya so…â€?. Fahimah ta ce, “I have a very short biography wanda ka fi ni saninsa. Na tashi na gan ni a duniya ban san kowa ba bansan komai ba sai AMMI. Don haka na shiga tsananin kidima da Ammi ta dauke ni ta baka Ya Uwais, babu wanda zai so dansa ya auri mara asali, ‘yar da ba a da tabbacin ko shegiya ceâ€?....â€?. Hawaye suka fito idonta, Uwais ya sa tafin hannunsa yana share mata ya ce, “You are a darling (ke abar so ce) ko da kuwa a ce daga sama ne ki ka fado, ba dan Adam ne ya haife ki ba! Ki yarda da ni Fahhimahâ€? and I promise you LOVE and protection till my last breadth. Ko kin ga iyayenki watarana, ko ba ki gansu ba har abada, Fahhima zan rayu da ke matsayin uwargidana kuma uwar 'ya'yan da zan haifa a gaba, daga gidan duniya har gidan aljannahâ€?. Kalaman Uwais sun narka zuciyar Fahimah, sai ta rungume shi sosai tana hawaye. Ta ce, “Ya Uwais na dade ina sonka, ina son kasancewa da kai, your odd behaviours ba su taba sanya min tsanarka ba. Kullum gaya wa kaina nake I didn’t deserve to be loved shi ya sa ka ke maltreating dinaâ€?....â€?. Uwais ya sanya tafin hannunsa ya toshe mata baki yana girgiza kai, ya ce, “Actually Fahhimahâ€? iâ€? I’m jeolous of you. Sabida son da Ammi ta ke miki, bayan wannan sai kuma ganewa da na zo na yi Ammi daga gidan marayu ta dauko ki, I’m sorry Fahhimah, amma ki yarda soyayya ba ta yin kanta, sai lokacin da Allah ya nufa. A yau na samu kaina dumu-dumu a so da kaunarki, wanda nake fatan har mutuwa ta dauke mu tare, mu tashi tare a aljannah matsayin miji da mata ranar gobe kiyamah…â€?. Fahimah sarkin kuka, kalaman Uwais sabida dadin da suke mata hawaye kawai suke sanya ta. Ba su suka bar gidan ba sai wajejejn karfe goma na dare, Amrah ta yi kira har ta gaji ba ta same shi ba don tun shigarsa gidan Ammi ya kashe wayar sa.