[16:09, 12/19/2016] Swtbaby: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 0⃣1⃣ *ANAS* K’auyen Bama dake jihar Maiduguri, Borno. Da yammacin ranan Asabar misalin k’arfe biyar da mintuna aka. Ruwan sama akeyi me ni’iman gaske, ga wani iskan dake hurawa me kad’a bishiyoyi da flawoyi, ko ina ya d’au sanyi. Tsit kukeji a garin, yara da manya, maza da mata kowa na cikin gdajensu, masu tafiya akan hanya kuwa sun faka gu d'aya, motoci dabasu fi a k’irga ba ke wucewa time-to-time. Can k’ark’ashin wata bishiyar ’yim na hango wasu samaruka guda hud’u wanda barasu gaza kuma barasu fi shekaru 17-18 ba. Daga nesa nake, amman hakan be hana ni tantance kyakkyawan cikin wad’annan samarukan ba. Wani kyansan ma sanda na gama k’arisowa, fari ne yellow shar da gashi kwance a duk sassan jikin d'an Adam da akasan na tsirar da gashi. Gashin kansa nada yawa saidai bawai afro tayi ba saboda tsantsin gashin bai tsayuwa, luf-luf yake kwance a kansa, bak’i k’irin yana yalk’i wane yasha mai. Saje ne kwance akan farar fatar fuskarsa wanda da ace yanada gemu da sun had’e. Gashin girarsa ba a cike take erin thick dinnan ba, silky yake a kwance d’an siriri wane yayi carving nasu. Dogayen eyelashes nasa wanda suke kallon k’asa santsi ne dasu. Bashida dara-daran idanunu, idanun nasa suna nan madaidaci da k’wayoyin idan nasa light blue wane na bature. Nasha jin ana cewa a Africans akoi masu blue eyes ban tab’a yarda ba sanda naga wannan saurayi. Hancinsa ma ba dogo har bakan nan bane, daidai yake cikin 'yar fuskarsa wanda yakasance shi ba dogo ba bakuma gajere ba. Bakinsa light red yake d’an madaidaici cikin fuskar tasa. Dukda cewar ya d’aure fuska hakan be hana dimple na kumatun damarsa lotsewa ba wanda babu hakan a na hagun. A zaune yake amman hakan be hanani tantace tsawonsa ba, dogon na miji ne, yanada faffad’ar k’irji duk da cewar siriri ne. Ofcourse ana cewa d’an Adam bai cika goma but za’a iya kiran wannan saurayi hallitar data cike goma bansani ba halan ya gaza ta hali amman inde ta hallita ne kam masha Allah, Allah yabasa, ban tsammanin akoi macen da zata ga wannan saurayi bata kuma kallonsa ba. I mean ba mace kad’ai bama kowa in all. Sanye yake da mint blue T shirt wanda ya mugun amsar farar fatarsa, jeans na jikinsa kuwa tad’an kod’e alaman tasha ruwa. Rik’e yake da kara a hannunsa yana wasa dashi da siraran yatsunsa wanda suke nan kan ba na miji ba. Gefensa saurayi ne me kama da shi sak, saidai komi na wannan kyakkyawan yafi nasa, kuma shid’in be kai kyakkywan fari da k’war jini ba, duk yadda akayi wansa ne na jini saidai na kasa tantance wane babba cikinsu. Sauran biyun k’arshen kuwa chocolate skinned suke, saidai still d’aya yafi d’aya haske. “ANAS na mata kenan!” Cewar d’an bak’i na k’arshen tare da kewayo da kallonsa kan kyakkyawan cikin nasun wanda nake da tabbacin shine ANAS d’in yana mai murmushi wanda hakan ya bayyano da brown teeth nasa, tabbacin kanuri ne shi kenan. “Uhm uhm fa BAANA!” cewar me haske na gefen d’an bak’in da yayi magana yanzun kenan. BAANA yace, “ah’ah barni in tsokanosa de.” Shide kyakkywan nasu da ake kira da ANAS be tanka saba, hasali, yi ma yayi kamar besan ana magana a gefensa ba se b’antare karan dake hannunsa yakeyi yana kallon yadda ruwan saman ke sauk’owa. Wanda nake kyautata zaton wan Anas d’in ne yace da d’an bak’in gefen nasa “barsa de KASHIM, neman magana yake yau gun ANAS.” KASHIM ya karkato da kallonsa kan BAANA “aikam naga alama rad’au a fuskarka, kuma wallahi kasan inya shak’ure ka bame k’wato ka, kasan halin mazan namu. Ko mata ma bai ragar masu ba bale kai,” ya d’an yi shiru sannan ya k’arisa “gardi” Yafad'a cike da gatsine. BAANA yace, “hummm zagen dai, naga kap nan gardawa ne har Shettima k’anin mun ma(k’anin Anas knan)” Duk suka k’yalk’yale da dariya illa shi wannan kyakkywa da suke kira da Anas wanda yayi burning face sekace besan me kalmar dariya ba. Niko miemie na matsu injiyo muryan wannan kyakkyawan da suke kira da Anas. Yawancin anacewa wanda yafiye kyan fuska bai fiye zaqin murya ba kuma hakan ne sanda na jiyo muryan Anas na k’aryata wannan batu. “You see, ruwan nan na tsayawa barama kuganni anan ba to talk more of kumin tsiya mtschww.” Cewar Anas tare da watso musu harara sekace mace. Lallai! Allah yayi murya anan, muryar Anas sautin na miji ne da anji amman saidai ba tattausar murya bace, zaqi ce ga me sauroro, bakuma zaqi erin ta mata ba saboda yadda muryar ke cracking a hankali in yana magana. “Toh Anas meyayi zafi daga fad’in gaskiya? Ai gaskiya ce wallahi kap ‘yan matan garin nan basu san wani na miji sekai, narasa menene kake dashi bamuda, ni da bansanka bama se ince asircesu kayi.” Cewar Baana yana nuna yadda abin ke damunsa. “Ahhh lallai Baana ka soma zarewa” cewar Kashim cike da mamaki. “Yanzu har seka tambayi ko mesa matan garin nan basu kula kowa se Anas? Bakada ido ne?” Shettima ya karb’esa “gaskia da alama.” Kashim ya cigaba, “k’warank’wasa ace yau ni mace ce nima sena so Anas wanga blue eyes sekace bature, ko ka manta teacher'n English namu da ke sansa.” Suka sake sheqewa da dariya at once kuma sukayi shiru suna jiran tsiwar Anas to thier suprise be ce masu ko uffan ba miqewa yayi da niyar tafiya dukda cewar ruwa akeyi fuskarsa a tamqe kwata kwata abin be basa dariya ba. “Haba maza yi hak’uri mana karka fad’a min cikin ruwan nan zaka tafi!” Cewar Shettima wansa tare da rik’o shirt na Anas. Harara Anas ya galla masa da nufin ya sake masa kaya, kafin ace me k’arfin ruwan saman ya dad’a k’aruwa ba yadda ya iya dole ya koma ya zauna. “Wai zanso inga Anas yayi aure wataran, muga ya zena controlling wannan uban temper'n nasa da matarsa.” Cewar Baana. Take Shettima ya juya ya kallesa tare da zaro masa ido yana me masa warning. Dukda cewar Anas be tanka sa ba amman fuakarsa takoma ja alokaci d’aya ya had’e girarsa gu d’aya kallo d’aya za’a masa asan ransa ya b’aci ko dan meh oho? Kodan kiran kalmar ‘aure’ da abokin nasa yayi ne? Cikin tsiwa yake maganar ba alamar walwala a tattare dashi. “Baana don't push it, nasha fad’a maka time without number bana san kana min maganan aure ko kuma ‘yan mata in muna tare, that goes to both of you” ya nuna Kashim da Shettima. “Banaso! Banaso! Inhar kuna sona yaci ace kundena for goodness sake!” Shettima ya dafe kafad’arsa “toh maza we are sorry.” kallonsa yayi ba tare da yace masa komi ba sannan ya kau da kai. Baana ya numfasa sannan yace, “toh ka fad’a mana why mana, kullum se kace bakasan kalmar aure ko budurwa amman baka tab’a gaya mana mesa ba, as friends we have to know ko bahaka ba Kashim?” Kashim ya giad’a kai “sosai mah kayi gaskiya.” Shettima kuwa dayasan mesa wan nasa bayasan wannan kalmomi guda biyu kawai ya kad’a kansa cike da nadama, yayi yayi ya ganar da d’an uwansa gaskia yakuma sa ya yafe wa mahaifiyar su amman ina abin ya gagara sam saboda abinda tayi ta sa Anas ya kariya, zuciyarsa a toshe take da bak'ar kiyayya is hardly aga Anas yana dariya, murmushin ma se in abu yakai ya kawo ne yakeyi. “I can't tell you guys, I'm sorry saboda talking about it makes me sick kawai ni kudena tareraya ta da wannan magana banaso give me a break please.” Baana ze sake magana Shettima ya dakatar dashi ta aza yatsa kan lips nasa. In akoi abinda yafi damun wannan abokai guda biyu, (Baana da Kashim) befi wannan halin abokin nasu ba, ace da an kira kalmar aure se mutum ya b'ata rai, aure da ta kasance sunnah me k’arfi wanda kowani d’an Adam keda burin cikata. Gaskiya da abun duba. Kashim yakasa hakura shikam sanda ya kuma tambaya “Anas munsan baka san maganan nan amman ka dage ka fad’a mana, who knows! we might be of help.” Juyowa Anas yayi ya kalle sa tare da wata murmushin takaici ta gefen lips nasa wanda a sakamakon hakan ya bayyano da fararan hak’waransa da suke kamar an daidaita tsawonsu “help? Hmmm, k’arshen k’ok’arin da zaku iyayi shine ku dawo da ita kuma koda kunyi hakan ma barinyi appreciating ba saboda tafita a raina, bana san sake sata cikin idanu na, ta cuceni ta cuci two siblings d’ina Shettima da Amal, and most of all ta cuci Abuu (mahaifinsu). I don't want her ever in my life.” Cike da mamaki Baana yace, “subhanallah wa kenan?” “Bade mahaifiyarku ba?” Kashim ya tambaya. Anas bece dasu komai ba Shettima ne ya giad’a masu kai da nufin eh mahaifiyar su Anas ke nufi. “Subhanallah! Subhanallah! Anas be kamata kana maganar mahaifiyar ka da ta kawo ka duniya haka ba, uwa uwa ce. Kome tayi maka ka tuna ita ta kawo ka duniyah.” “Thats my point!” Anas ya fad’a a masifanche. “Ita ta haifeni, ita ta kawo ni duniyah abin dayafi ban haushi fiye da komai kenan. Taya matar da ta kawo ni duniyah zata tafi ta bi wani na mijin daban ta bar family’nta a baya, How? Why? Mesa mata basuda tausayi? Mesa Allah yayi su mugaye masu san kai da abin duniyah mesa? Mesa basuda Imani? Mesa tayi breaking heart na Abuu haka? Har yau yakasa trusting wata ‘ya mace a duniya. Why does it have to be this way? Why? Mstchww!” yaja tsaki cike da haushi. “We are sorry” Kashim yafad'a cike da tausayi, so wannan grudge d’in Anas ke holding a zuciyarsa har yanzu saboda abinda mahaifiyarsa da Shettima tayi musu. Yau shekaru kusan bakwai kenan da sanin junansu amman be tab’a sanin mesa Anas ke cikin k’unci ba, kullum ba walwala a tattare dashi se yau. Tun ba yau ba yakeson jin me tarihin Anas amman Anas ko kad’an baisan maganar haka zalika ya hana wansa Shettima fad’a ma kowa. Yau d’inma halan saboda sun tak’ura masa ne yasa ya fad’a. Tun da suke a secondary school haka Anas yake, ko erin secondary school dating da akeyi d’innan Anas be tab’ayi ba hasali betab’a showing koda slightest interest akai ba ma. Unlike his brother Shettima daya d’au komi as k’addara yake living life nasa peacefully cikin walwala da dariya. Tunanin ya zeyi ya karkato da hankalin friend nasan kan gaskiya yake. Gyaran murya yayi sannan a hankalche yace “Anas we are all here for you, we are like brothers yanzu. Nasan how hard this must be for you amman dole kayi haquri ka rungumi qaddara kamar yadda Shettima yayi.” “No Kashim, I can’t baran iya ba. Karka had’ani da Shettima, Shettima was a small kid back then time da abin yafaru, definately ya manta komai bare iya tuna koda abu ba, but me? Da wayona da komai na wannan matar ta tattara kayakinta, we were all begging on our knees muna roqarta karta tafi... Mschww I don't want to talk about it banasan ciwon kai, you two have heard enough.” Anas ya fad’a tare da miqewa daga mazauninsa. “Finally ruwan ya tsaya” yayi qoqari canza topic d’in, yana miqa wanda a sakamakon haka joints na jikinsa suke sakar k’ara. “Shettima lets get going, yakamata mud’an taya Ummee da aiki kafin Maghrib yayi” (Ummee; k’anwar mahaifinsu wacce takasance tamkar uwa a garesu tunda mahaifiyarsu ta tafi ta barsu take kula dasu). Shettima ya mik'e shima suka d’anyi manly shake da juna, “alright! Se mun had’u a masjid” Anas yace da Baana da Kashim da suke zaune har yanzu sannan ya juya shida Shettima suka soma tafiya. “Huh!” Kashim ya numfasa, “ina tausaya wa abokin nan namu, like sosai. Zuciyarsa ta riga ta toshe da tsantsan k’iyayya.” “Sosai fa Kashim, but tsaya kaga wani abu yanzun nan ze dawo” cewar Baana yana murmushin jin dad’i. “Bade ya manta blessing d’inba?” (Yaren da masu shaye shaye ke amfani dashi wajen kiran ‘wiwi’). Baana yace, “Yup!” Tare da d’aga girarsa sama yana murmushi. *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [16:09, 12/19/2016] Swtbaby: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 0⃣2⃣ Tafiya suke a sahu d’aya, tsayin nan nasu na nan d'ai da kad’an Anas ya d’ara Shettima inba wai ance ya da k’ani bane za’a zata agemates ne. Daidai lokacin da suka yanko wata corner kenan Anas yasa hannu a aljihu yaji wayam ba komai, cak ya tsaya hakan yasa Shettima tsayawa shima. “Ya maza lafiya?” “Ba lafiya ba, go ahead I'll catch up nayi mantuwa.” cewar Anas. Shettima ya tsaya ya k’are ma d’an uwan nasa kallo sannan yace, “bade blessing d’in ba.” Anas ya kallesa da gira d’aya d’age sannan yace, “toh meh? Kadega yadda su Kashim suka sani tono maganan chan definately nasan ciwon kai ze kamani and despite that, yadda akayi ruwan saman nan I'm gonna enjoy sleeping.” tare da d’anyin murmushi wanda ya sake bayyano da kyansa tare da lotsar da dimple nasa dake kumatun dama. “Kona yau baraka hak’ura ba?” Shettima yasake tambaya. “Se in na amso karka sha” cewar Anas. Dariya kad’an Shettima yayi “zan d’an tab’a mana, naji ance da akoi dad’i cikin tea.” Anas ya dafe kafad’arsa “lets go?” Da d’aga kan da Shettima yayi suka juya suka dawo gun Kashim da Baana. Suna iso wurin nasu, Anas yace, “maza bani!” Baana yaci fuska “ban gane baka ba, mezan baka?” “Wai me ka maidani ne? Give me!” Anas ya fad’a a little bit pissed. Dariya Kashim yayi “basa please kaga har yafara losing temper.” Nan Baana yasa hannu a aljihu yaciro wata leda ya raba into two saidai d’aya yafi d’aya yawa sannan ya mik’a wa Anas kad’an din. “Are you serious? Naga fa wannan abu ni nasaya da kud’ina so kabani me yawan ko in hanaka duka.” Baana yace, “haba! Anas namu na kanmu, kap qauyen nan fa kai kad’aine me blue eyes yi hakuri mana. Aikasan da inada kud’i dana siya nima.” “Toh ni na hanaka yin noma ka samu kud’i? Abeg give me and stop wasting my time.” “Dan Allah fa nace” Baana yafad’a pleadingly. “Okay naji talaka kawai semun had’u a masjid then.” Daidai sunkai ga shiga corner'n gdansu kenan wata budurwa tafito daga wani gida, sanye take da hijabi iya guiwarta, dududu barata fi shekaru 15-16 ba. Idanunta suna sauk’a kan Anas ta sakar dawata murmushi. Tsuka Anas yaja yasa qaninsa a gaba yana tunkud’esa dan suyi sauri subar gun shiko Shettima daya gano haka tuni ya rage saurin tafiyarsa dukda tunkud’in da Anas kemasa. Se k’arisowa wajen nasu wannan budurwa ke. “Anas kamar kayi bak’uwa ko? Wannan ba Aisha bace? Ka tsaya kaji me zatace mana.” Cewar Shettima yana murmushi. “Wallahi in bakayi shiru ba zan mareka, kuma barakayi tafiya bane?” Daya wani tunkud’a gaba Shettima besan sanda yasoma matching dasauri sauri suka bar wurin ba. Isarsu gidah keda wuya suka tarar da Ummee a tsakar gidah tana tsince shinkafa. Da sallama suka shiga ta amsa da fara'arta. ‘yar dattijuwa ce wacce barata fi shekaru 45 a duniya ba, tanada haske sosai amman bara’a kirata da fara ba, ga kyau daidan gwargwado masha Allah!. “Ohhh mazan nawa sun iso ne? Sekuma ruwa ya tareku a hanya ko?” “Eh Ummee” cewar Anas yana k’arisowa wajen da take. “Me kikeyi haka?” “Tsince nake baba na, tuwon shinkafa Abuu keson ci gashi har ruwan ya tafasa ban gama ba.” “Toh Amal fa mesa bata tayaki ba? Anyways kawo in tayaki Ummee.” “Kai Baba na kaide Allah shi maka albarka” ta d'ago kai tana kallon Shettima dayayi kamar besan ma me suke fad’i ba. “Kai yanzu Shettima koda aiki ze taru ya kasheni ba ruwanka da bari ka tayani ko? Baka ganin wanka ne?” “Toh Ummee fisbailillahi ina aka san maza da tsintar shinkafa.” Baki wangalau ta bud’e tana kallon Shettima dududu shekarunsa sha shida ne fa da abu aka yake wannan tsiyar bayan ga wansa Anas me shekaru sha takwas bece komi ba. “Ehh hakane, sannu fa” tafad’i cike da gatsine. “Oyoyo Ya Anas” cewar wata kyakkyawar yarinyar da baratafi 8years ba fitowarta daga wata d’aki, ba shakka itace sistersu da suke kira da Amal, kyakkyawace sosai kamar sauran yayun nata bata gama kai Anas fari ba amman tafi Shettima. Su uku kap kamanninsu d’aya. (Bayan tafiyar mahaifiyarsu daga gdansu da wata takwas ta turo da Amal da wasiqa na cewa tabar gidan da cikin Amal ga ’yarsu nan ta haifota, kwanan ta d’aya a duniya kenan) sanadin haka Anas yake mutuwar san Amal duk rashin kunyarta bata masa saboda duk fitar da zeyi seya siyo mata abun k’walama unlike Shettima da cikinsa kawai ya sani thats the reason why basu shiri da Amal kullum cikin fad’a sukeyi duk sanda Anas yazo kuma seya bata gaskiya, wani sa’in har taran dangi suke masa. “Oyoyo my angel” yafad’i tare da bud’e hannunsa tazo da gudu tayi hugging nasa. “Ina sweet d’ina ya Anas?” kafin ya amsa mata ta zira hannu cikin aljuhunsa taciro ’ya’yan wiwin da Anas ya amso gun Baana sekuwa idan Ummee yakai kai. “Baba na meh wannan!?” Ta tambaya tare da zaro idanu waje. Nanfa Anas yasoma kame-kame can yace, “laaa Shettima kalli wannan abin da abokin Baanan can yace na rik’e masa” yama Shettima ido. Shettima yace, “ohh yamanta be karb’a ba kenan?” “Gashi anan kuwa!” Cewar Anas. “Anyways meh abun nema?” ya amshi daga hannun Amal. Ummee tace, “maza ka mayar masa wannan abu shaye shaye akeyi dashi, mayar masa maza!” “Toh Ummee amman bansan ina gdansu ke ba, agidansu Baana muka had’u.” “Nide koma me ka mayar masa.” “Toh Ummee bari in muka fita Maghrib zan bawa Baana ya mayar masa.” Anas yafad’i a hankali “Toh” tace tare da numfasa. “Ya Anas to ina sweet d’ina toh?” Cewar Amal. “Angel bansamu na saya miki ba, shops d’in duka a rufe I promise gobe kinji?” A hankali ta giad’a kai tare da turo baki. “Tsaya kiji wani batu” nan ya daidaita tsawonsa yakamo nata tare da rad’a mata wata magana a kunne aikuwa tahau tsalle suna ido hud’u da Shettima ta galla masa harara. “Wallahi Amal niba sa’anki bane wa kke harara? Maras kunya kawai.” Kafin Ummee ta masa magana Anas yace “ah’ah karka zagarmin k’anwa now go inside okay? Anyi ruwa kar mura ya kama ki.” Tana tsalle takoma ciki. Ba tare da b’ata lokaci ba Anas yataya Ummee suka gama tsince shinkafar banda Shettima daya tsaya kansu yana kallonsu cike da mamaki yarasa meke burge Anas a aikin kitchen bama aikin kitchen kad’ai ba. Bayasan ganin abinda ze tab’a Ummee ko Amal, he is so protective of them, duk abinda zeyi zeyi inhar it will keep them save and happy. ***** Bayan sunfito daga masallaci iyayensu sukayi gaba a yayinda Shettima, Anas, Baana da Kashim suke tafiya a bayansu suna tattauna warsu ta maza. Wata budurwa ce ta b’ullo gabansu, dakatar dasu. “Ina wuni?” ta gaishesu duk suka amsa illah Anas dake neman any chance yabar wajen. “Anas ina wuni?” tasake fad’i cikin wata anniyar murya ganin shine be amsa ba. Shiru yamata, “Shettima ko nama Anas wani abu ne baimin magana?” Murmushi k’adan Shettima yayi sannan yayi k’arya “ko kad’an Hafsah mura yake saisa bai iya magana.” Wani kallo Anasa ya watsa masa wanda shi Shettima yamayar da murmushi. Kafin yace wani abu Hafsah tace, “dama zuwa nayi na tayaka murna ne kan scholarahip daka samu cewa nanda ‘yan kwanaki zaka London shine na had’o ma wannan pepper soup sekuma gashi kana mura I'm sure ze d’an wassakar maka da muran ma. Gashi please ka amshi” Ganin Anas baida niyan karb’a Shettima yasa hannu ya amsa “kai sannu Hafsah kamar kinsan mura na damunsa kika kawo wannan.” Shettima ka tabatta Anas yasha please ze taimaka masa sosai.” “Aii karki damu” cewar Kashim “consider it done, zamu tabbata yasha.” Da murmushi a fuskarta tace, “toh nagode seda safenku.” Sanda ta sake kallon Anas sannan ta fice. Nan Anas ya finciko Shettima tare da kama masa kunne ya murd’a da iya k’arfin da Allah ya basa. “Awchhhh!” Shettima ya sakar da k’ara. Karb’e kulan abincin Anas yayi ya soma tafiya. Baana yace, “ya haka kuma? Nad’au ai baraka ci ba.” Duk suka k’yalk’yale da dariya. Bece dasu komi ba yacigaba da tafiya, “anji kunya” cewar Shettima nan ma be tankasu ba. Yana isa gida ya tarar da Ummee tana ‘yan wanke-wanke kafin ya b’oye flask d’in har ta riga ta gani. “Baba na me wancan kake k’ok’arin b’oyewa?” Cewar Ummee da murmushi fal a fuskarta. “Oh wannan!” Ya d’ago flask d’in sama “erm... Erm... Na-” “Iyye baba na manya har ‘yan matan naka sun soma kawo maka abinci ne, to yayi kyau. Me aciki?” Kamar ya mata k’arya sekuma ya fasa, “pepper soup ne nakawo wa Amal ko kema zaki tab’a?” “Noo haba! Budurwa takawo wa Baba na kaji kuma se inci je kaci abinka.” “Kai Ummee da Allah bafa budurwata bace.” “Hehe!” tayi dariya sosai “yanzu uwar taka kake jin kunya?” Rashin sanin me zece mata yasa ya wuce ta kawai ya kira Amal suka wuce d’akinsu ya bud’e masu suka sha pepper soup nasu. Ni miemie nace Anas ba kunya yanzu sha yake!? Lol Sun ci kusan rabin kazan Shettima yashigo senishi yake da alama gudu yayi ya iso nan. “Yanzu Anas cinye kazan nan zakayi da wannan maras kunyan baraka d’an bani ba nima?” “Eh bara'a bayar ba” cewar Amal “Ya Shettiman nan shegen kwad’ayi wallahi ko Ya Anas?” Ta sake p’antarar kazar ta kai baki. “Sosai ma Angel” Anas ya amsata. “Wallahi Amal ki kiyaye ni” gwalo ta masa sanin in Anas na gefe da ita ba abinda Shettima ya isa ya mata. “Ka kwantar da hankalinka bari mu fita sallan Isha har gidansu Hafsah zanje in fad’a mata ka cinye kazan kap ko k’ashi baka bari ba.” Murmushi kad’an Anas yayi “to ai ko ka fad’a mata ba yadda zatayi ba saboda ban bata fuska ba.” Haka ya dake sanda suka cinye kazan tas shida Amal, pippike da wuya suka ragar sannan Anas ya ceda Amal ta mik’a ma Shettima da yawunsa ke d’iga k’asa. Itako ta d’aga ta ajiye mai “gashi Ya Shettima.” Hannunta ya rik’e tare da danna mata nank’washi aiko tasaki kuka harda na munafirci take Anas ya k’ariso ya rama mata. *** Haka ma da suka dawo sallan Isha Aishar d’azu ta tsaresu tare da masu sallama kap suka amsa illa Anas. Sak batun da Hafsah tayi haka Aisha ma tayi sede nata chips da omalet ne, itama na taya Anas murnan samun scholarship da yayi. Anas na jiran Shettima ya amsa kamar na d’azu aikuwa yak’i. “Dan Allah kayi hak’uri ka karb’i Anas ni badan kasoni na kawo ma ka ba, consider it as a friendship gift please.” D’ago blue eyes nasa yayi ya kalleta ciki ciki wanda tuni ta soma shaking tare da kawar da kanta. Ajiye flask d’in tayi a k’asa “dan Allah ka d’auka se da safenku.” Aiko tana shigewa cikin gdansu ba kunya Anas ya d’aga yakama tafiya. Baana yace “andeji kunya” haka suka ta masa tsiya amman ko a kolan rigarsa, duk yasan so suke suci kuma bayarwan ne bareyi ba. Nanma dashi da Amal ne suka cinye wannan karan ko ragowar ma ba’a baiwa Shettima ba. **** Da misalin k’arfe goman dare bayan kowa ya kwanta a gdan. Anas da Shettima suna kwance kan seperate gadonsu bayan sun gama shan wiwinsu cikin tea. Shettima daya zura wa Anas kallo na kusan mintuna yace, “tunanin me kake haka?” “Anas?” Nanne ya dawo hankalinsa “yes! kace me?” Shettima ya kuma nanata kansa “nace tunanin me kake?” Murmushi sosai Anas yayi wanda yasa dimple nasa lotsewa sosai, kad’an daga cikin fararen hakwaransa suka bayyano. “My dreams are about coming true.” “Wani dream kenan?” Shettima ya tambaya tare da tasowa ya zauna kan gadonsa tare da jingina bayansa a jikin kan gadon. “Don't tell me bakasan dreams d’ina ba! Ofcourse to be a billonaire se in samu inyi breaking hearts na thousand of women by then kaga na ramawa Abuu abinda mamarku ta masa.” “Wai wace erin magana kakeyi Anas? Wai yanzu kana ganin in Abuu yaji wad’annan munanan kalamu daga bakinka zeji dad’i? Haba mana kai baka yafiya ne?” “Yafiya! Har yau bansami defination na word d’in a dictionary ba plus in wa’azi kakeson yi kaje masallaci kayi, kagannin nan? Banasan jin wannan wa'azi allow me to get some sleep yadda nasha ’ya’yan wiwin nan.” Nan yaja bargo tare da rufe kansa ciki a hankali bacci me nauyi ya daukesa. *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [16:09, 12/19/2016] Swtbaby: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 0⃣3⃣ *FANNAH* ‘kauyen Bama dake jihar Maiduguri, Borno. Kyakkyawar budurwa ce zaune cikin wata ‘yar k’aramar d’aki bisa gaban wata ‘yar madubin da aka mak’ala a jikin bango. Ba komai bane a d’akin illa katifan dake shimfid’e a k’asa seda bakunan sa kaya da leather carpet ciki. Ba shakka basu da arziki. Dududu wannan ‘yar budurwa baratafi 15 years old ba. Tanada haske sosai, da sirirn hanci dakuma plumpy lips, idanunta ba laifi ‘yan manya ne dadai. Gashin girarta acike yake mekyawun gaske ba ruwanta da zana artificial gira [ba erinsu ni ba;( ] in kuwa aka k’are mata kallo sosai za’a ga alamar had’ewar girar ta guda biyu gu d’aya sede be munanta taba hasali kyau ma yak’ara mata. Gashin idanunta a cike suke kuma dogaye, saje ne a fuskarta kwance luf-luf wane na miji (kaman nawa, lol) gashin kanta dana girarta sun had’e dan yawansu. Hannunta gashi ne a kwance dogaye masu mugun kyau. Siririya ce de tanada tsawo daidan shekarunta, tana sanye da wata atamfa maroon da torches na white and green, se murza wata ‘yar jan baki pink take a lips nata hankalinta kwance da anganta ansan batada matsala. A lokacin da wayarta k’irar Nokia Asha dake kan cinyarta tayi k‘ara, a hanzarce ta duba tana ganin sunan daya bayyana kai _Ya Ahmad_ tayi murmushin jin dad’i sannan ta bud’o sakon ta karanta kamar haka; _my Fannah I'm outside waiting for you yanzu shigowa na gari ko gida ban lek’a ba just wanted to see you_ “yeyy!!” Ta fad’a a fili tana murna. Data gama sa jan bakin ta shafa powder tareda sa kwalli a fararen idanunta take ta dawo wata balarabiya. A garin mike’wa d’an kwalinta ya since ya fad’i k’asa tare da ribbons data k’ukk’ula gashin nata dashi. Fans ko kunsan ya gashin buzayen Maiduguri yake? Erin bak’i k’irin me santsi da tsawo kamar haukan nan? Haka gashin wannan ‘yar budurwa yake. Ni kaina miemie dana gani sanda na tsorata dukda cewar ita kad’ai ce a d’akin hakan be hanata yin saurin tattara ribbons d’in gu d’aya da sauri ba tasoma k’ok’arin faka gashin nata gu d’aya saidai dan cikar gashin ta kasa, hannun nata suna nan sirara ba fad’i ga uwa uba gashi har tsakiyar bayanta. Kamar wacce zatayi kuka tafito d’akin “Mami! Mami!” Shiru kukeji wani mutum ne wanda bara’a kirasa da dattijo ba danko befi shekaru irin 44-45 dinnan ba ya lek’o daga wata d’aki wanda ya kasance opposite daga d’akin da Fannah tafito da alama mahaifinta ne dukda cewar basu kama kuwa. “Fannah uwata ya akayi? Tsaya mesa kike yawo da kanki a bud’e haka?” Kamar wacce zatayi kuka tace, “Baba ribbon d’in ne yafita kuma nakasa d’aure gashin, Mami nake nema ta tayani.” “Shine zakiyi kuka uwata?” Cewar mahaifin nata “Mami batanan tashiga mak’ota.” “To baba Ya Ahmad fa yazo yana jirana a waje ko gida be wuce ba ya zosa nan.” “Oh! Keda Ahmad d’inkin nan se Allah. Ina Afrah da Aiman toh?” “Sun tafi islamiya Baba.” “Yoh! Kekuma fah?” “Kai Baba wai yanzu so kake kace ka manta sauk’an nawa? Abinda har Hajji kaje da kujerar da aka bani danayi na biyu.” “Haka fah, taho to in kama miki kan.” “ Yawwa Baba na.” Da gudu taje ta zauna gabansa shima sanda yayi dagaske sannan ya kama uban gashin nata gu d’aya. Banda tsawon gashin gu d’aya. Wawan cika ne dashi saisa Fannah batta iya kamawa. “Toh nagode Baba.” “Yawwa ‘yar akbarka se ganin Ahmad ko?” Ta giad’a masa kai. “Ki sa hijabi fa tukun kuma kice ya gaishe min da mahaifinsa naji wai ya d’anyi rashin lafiya kwana biyu kuma ban samu na lek’a sa ba.” “Toh Baba zan fad’a masa in shaa Allah.” D’akinta takoma tad’au wata maroon hijabi wanda ya sake ciro da hasken ta tasa, tare da d’aukar wayarta sannan tafito waje idanunta suna sauk’a kan Ahmad nata ta sakar dawata murmushin jin dad’i. Ahmad saurayi ne me k’imanin shekaru 23. Chocolate skinned yake, yana da kyau dadai gwargwado gasan murmushi. Tsayyayen na miji ne masha Allah! “Ga sarauniyata ta fito.” Ya fad’a yana mai murmushi. “Gaskiya wankan nan yayi kyau sosai Fannah, kin ganki kuwa? Looking so take away.” “Ya Ahmad kaide kullum seka riga zolayata. Ina wuni? Ya hanya? Gashi ko ruwa ban samu na d’auko maka ba duk na k’osa in ganka.” “Laaa ai sarauniyata bata laifi ae, karki damu ni ganinki kad’ai ya kashe min k’ishi.” Hannu tasa ta tare fuskarta a kunyance. “To ya Ahmad mu zauna anan mana kar ka kaji a tsaye.” ta nuna wat benchi. “Haka sarauniyar tawa tace? “Haka to za'ayi.” Bayan sun zauna Fannah tace, “ya hanya toh? Ya makarantar?” Hannu yasa ya dafe goshi sannan yace, “so hectic fa Queen, biochemistry akoi wahala. Ga Maiduguri zafi like hell” “In shaa Allah ka kusa gamawa, Allah baka sa’a yaya na.” “Ameen sarauniyata.” Kefa ya school ‘yan matan ss2 koh?” “Kai yaya! School alhamdulillah” Ta fad’a tana murmushi. Hira suka d’an tab’a na ‘yan mintuna. Shi Ahmad ba abinda yake sake jan ransa kan Fannah kamar san addininta dakuma yawan yarintar ta dakuma sa sa dariya da takeyi in suna tare. Fannah batta magana d’aya biyu seta sa alhamdulillah, subhanallah, masha Allah ko jazakallahu bikhair ciki. Yarinyace me tarbiyan gaske, ga hankali da girmama na gaba da ita koda wasa bata tab’a kiransa da sunansa gatsau ba dole seta sa yayan nan kuma bawai they are related bane tsantsan girmamawa ne kawai. “Toh yaya na kar na ta jan ka da surutu nasan su Mama duk suna jiran ganinka, kaje gida ka huta.” “Toh sarauniyata” hannu yasa cikin jakarsa yaciro wata leather sannan ya mik’a mata. “Me wannan kuma yaya na?” ta tambaya suprisingly. “ ‘yar tsarabar Maiduguri ne nace barin kawo wa sarauniyata, yi hak’uri ba wani abu me tsada bane.” “Yanzu yaya karatu kakeyi amman seka rik’a kashe kud’inka a kaina? Ni gaskia kadena banso nafison kana kula da kanka a school.” “Ko kad’an Fannah baran iya zuwa nan ba tare da na kawo miki komi ba. I prmise you this duk sanda na fara earning salary’n kaina I will spend it on you, ina sonki sosai Fannah ta.” “Nima ina sonka yaya na. Nagode sosai, jazakalllahu bikhair Allah taimaka ya baka sa’a yaya.” nan ta mik’e. Mik’ewan yayi shima “ameen my Fannah inasan addu’o’in ki agareni, ba k’aramin taimaka min suke ba.” Ai saisa kullum nake including d’inka cikin prayers d’ina. Baba na naka sannu dazuwa also, yace ka mim’a gaisuwan sa gun Abba da jiki” Toh my Fannah, I'll tell him so se munyi waya ko?” kai ta giad’a a hankali. Wai! Ai na manta kun kusa fara exams ma, barinso jn hana Queen d’ina karatu ba” “Haba mana yaya ko wayan minti ishirin baramuyi ba?” Da murmushi a fuskarsa yace ai baki tab’a neman abu kirasa guna. Allah kaimu daren toh” “Yawwa yaya bo-bye” tamasa murmushi. Murmushin ya mayar mata “bo-bye Queen.” Ahaka tashigo ciki. Tun kafin ta yo d’aki ta soma bud’o ledar, abaya ce me kyan gaske ga stones kota ina. Wowww kukeji tana fad’i kamar Ya Ahmad yasan yadda nakeson abayah. Nan ta hau gwada wa kan kayarta bayan ta cire hijabin nata. Aiko daidanta tazo gwada yafa gyalen se kud’i ya fad’i daga ciki tana irgawa taga dubu biyar. Yanzu Ya Ahmad wannan d’inne zece ba yawa. Baba! Baba! Ta k’olla masa kira tana nufo d’akin nasa. Ya akayi uwata ta kaina? Ya tambayrta a kiabingid’e tare da kashe radio’n dayakw ji. Wannan kaya fa daga ina? Masha Allah Ya Ahmad ne yakawo min yanzu kaga harda dubu biyar kuma. Kai Allah shi mashi albarka, shi kullum cikin wahala yake miki? Gashi ko kayan yamiki kyau kka fito kamar balarabiya. “Kai! Baba dagaske?” Ta tambaya tana tsalle. “Sosai ma kuwa uwata.” ya amsata. Nan ta irga dubu biyu ta mik’a masa “gashi Baba ka rik’e wannan, Mama ma dubu biyu nida Afrah da Aiman kuma semu raba wannan.” “A’a uwata rik’e abinki kinji? Ki saya abubuwan da bakida dashi” ya mik’a mata. “Baba ni komai danake buk’ata inadashi ka karb’a kaji? Ko cafani sekayi dashi.” “Toh nagode uwata, Allah miki albarka ya cigaba da kare min ke.” “Ameen Baba zan koma d’aki.” Nan ta fice, isarta d’aki bada jimawa ba k’annenta Afrah da Aiman suka dawo. Atare suka shigo d’akin d’ayan tana nan kamar Fannah baratafi 13 years old ba whereas d’ayan kuma dududu intayi shekaru shine 3. “Ke wai Aiman kullum ne sekin tsaida mu akan hanya da sunan fitsari?” cewar 'yar babban (Afrah) kenan. “Anyin!” cewar Aiman yarinya ‘yar shekara uku se uban baki. “Ni kike ma rashin kunya? Iyye?” Fannah dake kwance kan katifa tana karatun History ta d’ago ta zauna “wai ke Afrah me damuwarki? Shikenan yarinya bara tayi fitsari ba?” “Ya Fannah ni ban tsoma bakinki ba, nida Aiman nake magana.” “Aww rashin kunya zakimin? Dama d’azu Ya Ahmad yazo ya bani kud’i nayi niyan baki kad’an daga ciki amman tunda rashin kunya zakimin na fas-” Afrah ta katse ta, “a’a yi hak’uri Ya Fannah ta.” Da gudu ta haura kan katifar “yaushe Ya Ahmad d’in yadawo?” “D’azu bakiga abayan daya kawo min ba!” Nan ta mik’a hannu taciro daga cikin wata bako take Afrah data kusan kamota tsayi ta amshi zata soma gwadawa Fannah ta k’wace “kefa bakida seti, akawo min kaya kiwani ce zaki gwada?” “Su Ya Fannah manya masu samari.” “Samari? Ai Ya Ahmad ba saurayi na bane miji na ne, kinga yana level 5 yanzu ina ss2 ina ss3 yana neman aiki ina gamawa se muyi aure by then yasamu aiki in shaa Allah” “Ahh lallai fa soyayya ruwan zuma. I'm envious.” Cewar Afrah. “Don't be, kema lokaci ne beyi ba Allah ze had’aki da mijin dayafi Ya Ahmad sona.” “Allah sa!” Afrah tafad’a da sauri “Ameen habibti” cewar Fannah. **** “Fannah! Fannah! Zo da sauri da Allah” kirar Mami. “Na’am Mami gani zuwa.” Sunnah take da niyar yi kafin tayi nafilar Maghrib kasancewar lokaci ya kusa yi amman dan kirar Maminta ta fasa tajeta. “Gani Mami” “Fannah yi hak’uri ki siyo min maggi ashago nan kusa wallahi bansan ya akayi ba har ya k’are ban sani ba yi hak’uri kinji mamana?” “Yanzu Mami aike zakiyi shine sekin had’ani da Allah harda bani hak’uri. Ina kud’in?” Nan Mami taciro hamsin ta mik’a mata. “Kinga ai kece babba Afrah yakamata in aika amman shegen yawonta tashiga nan mak’ota ganin jaririyar da Ameenatu ta haifa.” “Ayya ba komai Mami barin yi sauri kafin su rufe shagon.” “Toh Allah kare.” “Ameen” ta amsa sannan ta fice. *ANAS* “So Anas sauran ka 3 days kafire London kenan?” Cewar Shettima suna zaune a kan wata benchi a bak’in k’ofar gidansu. “Gonna miss me?” Anas yafad’a yana d’aga gira. “Eh mana I will miss you, nide Anas wallahi ka canza tsoron zuwanka London d’innan nake nan da Bama ma kana shaye shayenka a b’oye bale ace kaje can inda ba idan kowa.” “Toh yau kuma wa’azi zaka min? Kagannin nan yanzu haka akoi inda mukayi appointment da su Baana I will have my last drink a Bama yau kasan gobe zamu wuce Maiduguri, so kaga dole in sha in bugu tunda na k’arshe ne.” “Amman kasan Abuu nagari ko? In ya ganka a buge fah?” “Make up stories for me then, kamar yadda ka saba kace masa fad’a mukayi da wani. I'm going now.” “Toh masallaci fah?” Cewar Shettima. “Sena dawo zanyi sallar.” Daga nan ya fice inda suka saba had’uwa in zasuyi shaye shayensu ya je chan suka bugu like never, ko sanin ina suke in aka tambayesu ba sani zasuyi ba. Daidai Anas ya tashi ze tafi gida kenan aka soma wani erin masifaffen ruwa ba yadda Baana basuyi dashi yajira ruwan yad’an tsaya kafinnan ma hankalinsa yad’an dawo jikinsa ba amman sam yak’i jinsu ana ruwan yasoma tafiya, yazo ma besan ina yake dosa ba dan yadda ya bugu. **** *FANNAH* “Oh No! Shagon Ya Wakil a rufe gashi Mami battada maggin da zata yi amfani dashi dole in k’ara gaba” haka tatayin gaba duk shagunan a rufe amman still bata hak’ura ba. Bada jimawa ba aka soma ruwa me k’arfin bala’i gashi daga can tana hango wata shago a bud’e ta koma gida ba maggin kuma battaso. Cikin ruwan ta cigaba da tafiya daidai ta shiga wata lungu taga wani na miji daga gani a buge yake, duda acikin duhu ne hakan be hanata tantance kyansa da blue eyes nasa daya d’ago yana kallonta ba. Take ta soma b’ari Allah sa ba gamo tayi ba. Mutum da blue eyes. Addu’o’in kariya tasoma yi jikinta se rawa yake gu d’aya ta tsaya jiran yazo ya wuce tayi gaba itama. Daidai yazo kusa da ita seya tsaya hannu ya d’aga yakai kan fuskarta tuni Fannah ta soma kuka tunda take ba d’a na mijin daya tab’a tab’ata inba Babanta ba. Ga k’arfin ruwan saman koda tayi ihu bame jinta shagon data gani a bud’en ma har sun rufe. *©miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [16:09, 12/19/2016] Swtbaby: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 0⃣4⃣ Cikin kuka tace, “dan girman Allah bawan Allah kayi hak’uri I beg of you please.” Jikinta se rawa yake tana hawaye. “Bawan Allah dan Allah kayi hak’uri I'm just 15 ba abinda zan iya baka have mercy on me please dan Allah.” Ko k’adan be saurareta ba hijabin jikinta yasoma k’ok’arin cirewa. “Wayyo Allah Mami na! Baba! dan Allah kuzo ku taimakeni! ihu take sosai.” Hannu yasa ya rufe bakinta. “Duk mata haka kuke, mesa zanji tausayinki? Data gudu tabarmu ta tausaya mana neh? Why will I have mercy on you? I hope you tell her abinda zan miki yanzu saboda itama ta d’and’ana little daga cikin bak’in cikin data sanyamu time da ta tafi ta barmu” Yana d’aga hannu daga bakin nata ya yaga hijabin nata into two. Ihu ta sake sakarwa “bawan Allah dan Allah kayi hak’uri karka lalatani dan girman Allah, kaji tausayi na I'm just 15 years dan Allah ka rufa min asiri karka b’ata min future” “Data tafi ita taji tausayin mu ne?” A rikice bakin ta na rawa tace, “ww..wa ce? Ni bansan wacce kake fad’a ba bawan Allah ban tab’a ganinka ba seyau kayi hak’uri dan Allah, karka lalata ni.” Be saurareta ba ya yaga kayanta. Nan ta shiga tare k’irjinta kuka sosai Fannah takeyi tana rok’an wannan bawan Allah'n haka ba tausayi ba inani yayi raping (fyad’e) nata. Tun tana iya jure zafin har ta sume wajen, kaca-kaca yayi da ita sannan ya fice yabarta ruwan sama ma dukan sumemmiyar jikinta. Shi kansa besan ya akayi ya isa gida ba a daren, kawai ganin kansa yayi bisa kan gado. A hankali ya bud’e blue eyes nasa wansa Shettima yagani a kansa. Tunanin meya faru yakuma yake nan ya soma lokacin da aka soma ruwa yace dasu Baana ze tafi sukayi k’ok’arin hanasa amman ya k’i jinsu ya hau tafiya can cikin wata lungu.. Wata lungu... Daga.. Can kwata kwata seya kasa tuna meya sake faruwa. “Anas how are you feeling? Sanda na fad’a maka karka bi su Baana kak’i kasan yadda ruwan saman nan yamaka duka kuwa? In akayi wasa seka kamu da mura.” cewar Shettima fuskarsa a d’aure “Ina Abuu?” Anas ya tambaya. “Ka gode wa Allah be ganka ba sanda nashigo dakai nan. Anas fisabilillahi mesa baraka rungumi k’addara ka manta da zancen Ummimi (mahaifiyarsu) a rayauwarka ka yafe mata ba? You're blaming yourself for her mistakes, misleading your life in the process. Haba mana Anas. Saboda Ummimi kasoma shaye shaye me haka please? Yanzu saboda ita ka kusan kashe kanka, abinda tayi ya riga ya wuce se mu rungumi k’addara mu barta da halin ta.” “No Shettima I can never do that, tariga ta juya min rayuwa, my life can never be normal kamar yadda kakeso, I can never move on barni haka kawai inta misleading rayuwar nawa har zuwa sanda zan mutu. Images of yadda ta tafi ta barmu will never leave my head, they are stuck in it forver” “Anas wai kai mesa bakajin magana ne ko dan ni k’aninka ne kafisan babba ya maka magana? Bari Abuu ya dawo I think is about time yasan gaskia shima, I've been keeping your secret for how many years now? A ganina with time zaka mance komai amman tunda you are not ready to change, tunda baka iya rungumar k’addara ba zan fad’a wa Abuu komi idan ya dawo.” Sede daya juyo ya kalli Anas yaga ko k’adan ma hankalin sa ba a gunsa yake ba, yayi nisa cikin duniyar tunani. “Anas?” Ya kira sunansa. Shiru Anas yayi be amsa ba dan haka ya d’an jijjik’a sa. “Yarinyar...” Anas yace fuskarsa cike da damuwa. Se yanzu ya tuna yaga wata yarinya acikin lungun. Amma sam ya kasa tuna ya fuskarta take ko fara ce ko bak’a ko kyakkyawa ko munana, ko doguwa ko gajeriya shide yasan yaga yarinya cikin lungun. “Wata yarinya kuma Anas? Yau kai ke kirar mace cikin gidan nan?” “Yarinyar Shettima ina take?” “Wai wace yarinya Anas, me kake fad’i?” Shettima ya fad’i fuskarsa cike da mamaki “Yarinyar Shettima, ina take? Ina ka tsince ni?” Cewar Anas. “Can gaba da gidan gona and also meya sami kayanka duk jini na duba ka banga ciwo ba.” “Jini fa kace? Ina kayan nawa?” Anas ya fad’a a rikice. “Na wanke already.” “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un.” Abinda Anas keta nanatawa kenan duk yasa Shettima kid’imewa. “Wai meke faruwa ne Anas? Wani abu ne?” “A’a nothing thanks please in baraka damu ba I want to be alone in d’an huta thanks.” Shettima na fita Anas ya rufe ido so yake ya tuna fuskar wannan yarinya amman ya kasa, “ina take? Mena mata? Mesa Shettima yace yaga jini ajikin kayana. Oh no! Nayi blaming yarinyar da batasan komi ba akan laifin da Ummimi tayi. Oh no! Nayi raping d’inta subhanallah shikenan nazama mazinaci, Ummimi baran tab’a yafe miki ba abinda kika min, kin cuceni” Dakyar bacci yayi gaba dashi... **** *FANNAH* “Malam wallahi aiken maggi nan shagon bakin titi nace taje mun kuma har yanzu bata dawo ba, wayyo Allah inaji a jikina abu yasamu Fannah tah.” “Maman Aiman ki kwantar da hankalinki Fanmah yarinya ce me hankali tasan abinda takeyi barata tab’ayin abinda zesa mu cikin damuwa ba.” “Abin da nake nufi kenan Malam” Mami ta fad’a cike da tashin hankali. “Fannah bara ta tab’a yin abinda ze samu cikin damuwa ba saidai in za’a tilasta mata.” “Me kike nufi kenan Maman Aiman?” “Malam wallahi ji nake a jikina Fannah ba lafiya ba wayyo Allah tun kafin Maghrib fa na aiketa yanzu har Isha bata dawo ba, Allah ba lafiya ba nashiga uku!” “Maman Aiman ki kwantar da hankalinki yanzu d’auko hijabinki ga lema anan muje mu duba nan mak’ota ko halan tashiga tana jiran ruwan saman ya d’an saurara.” Nan ta d’auko hijabi sunzo fita kenan Aiman ta fito daga d’aki “Mami ina zakuje?” Idan Mami cike da hawaye tace, “nemo Ya Fannah zamuyi Aiman, bata dawo gida ba tun d’azu” daidai lokacin Afrah ma tafito “zan biku Mami.” tace idanta cike da hawaye tunda take bata tab’a shiga tashin hankali kamar na yau. Fannah ba mutumiyar yawo bace, ba inda take zuwa banda boko tunda ta kammala haddan Al~Qur’aninta. Dole ne wani abu yasameta a hanya, fatansu Allah sa ba sharri bane. “A’a Afrah ki zauna da Aiman a gida in shaa Allah yanzu zamu dawo.” “Mami what if something bad ya samu Ya Fannah fa? Please kibarni inje” tafad’a hawaye na tsiyaya a idanunta cike da tausayi da tsoro. “In shaa Allah ba abinda ze sameta” cewar Baba “ku zauna yanzu zamu dawo.” “Toh Allah kare” Afrah tace. “Ameen” Mami da Baba suka amsa a tare sannan suka fice cikin ruwan sama. Aiman ce ta rik’o hannun Afrah, “Ya Afrah me ze samu Ya Fannah?” Murmushin dole ta k’irk’iro “in shaa Allah ba komai karki damu kinji? Ya Fannah will be alright.” *** “Malam suka ce Fannah bata shigo nan ba innalillahi malam dan Allah ina zataje? Ina aka kaimin ‘yata?!” “Maman Aiman panicking is never a solution kizo mu dudduba kusa ko zamu ganta cikin shagu nan bakin titi” Haka fa iyayen Fannah suka ta duba sak’o sak’on unguwar tasu ba Fannah ba alamarta har sun fidda rai se Mami ta tuna shagon dake gaba da wata lungu a sabuwar unguwa tace suje su duba, sunayin wajen kuwa sega Fannah kwance a k’asa half naked ruwan sama yamata tsinannen duka ko numfashi battayi. “Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!” kawai ke tashi gun both Baba da Mami were shocked hawaye gangara suke daga kumatunsu suna kallon yadda aka walak’antar masu ‘yarsu. Mutuwan tsaye Mami tayi Baba ne yayi k’arfin hali yaja zanin ta dake gefenta ya rufe mata jikinta dashi tare da rungumota yana kiran sunanta sam bata amsa ba dake ko numfashi battayi. Alokacin Mami ta sakar dawata erin k’ara “FANNAAAHHHHH!!! WAYYO ALLAH!” Da gudu tayo kansu tare da jefar da leman ta karb’e Fannah tareda rungumota tana kiran sunanta “FANNAH! FANNAH! Dan Allah karki tafi kibarmu dan Allah kitashi wayyo Allah!” Kuka kenan! Mota Baba yasamu da k’yar aka sa Fannah ciki suka wuce babban asibitin dake hukumar Bama. Nan take akayi emergency da ita sam Mami ta kasa daina kuka shikansa Abba kuka yakeyi duk yadda yayi ya hana kan sa kuka ya kasa. Hannun Mami ya rik’e yana bata hak’uri tana kuka tace, “mesa Malam? Mesa se Fannah ta za'ai wa haka? Hankalinta yayi yawa ace an mata wannan tsiya. Malam shikenan an rusa wa ‘yata future Allah ya isa ma duk wanda ya mata wannan d’anyen aiki barin tab’a yafe wa ba...” ta fashe cikin wata erin matsanancin kuka. Rungumota Baba yayi yana bata hak’uri shima yana kukan. “Nima kaina abinda ke d’aure min kai kenan, wani azzalimi ne kawai yayi taking advantage na innocence nata saboda Fannah bawai tana mu’amala bane da maza bale ace saurayi ne yamata wannan abu, Ahmad ne kawai ke zuwa wajenta kuma nasan Ahmad bare tab’a aikata mumunar abu kamar haka ba.” **** _3 hours later_ K’ofar d’akin da Fannah ke ciki ya bud’u likita ya bayyana daga bayansa. Da sauri su Mami suka taresa. “Ya ‘yar tamu likita ya jikin nata?” cewar Mami da Baba a tare. Kai ya k’ada a hankali fuskarsa cike da tausayi. “Likita dan Allah karka fad’a min ta rasu, dan girman Allah” Mami ta fashe da kuka Baba yana bata hak’uri. “Iyayen Fannah kuyi hak’uri amman munyi duk iya abinda zamu iya dan ceto ran ‘yarku, mun kasa, ya gagare mu, mun kasa at all ruwan saman ya mata duka sosai har na fitan hankali, yabi ta kunnenta da hanci har baki, bayan haka kuma ga raping nata da akayi wanda aka mugun ji mata ciwo. Zafin datayi witnessing yafi k’arfin jikinta yafi k’arfin shekarunta. Yarinya ce sosai. Kuyi hak’uri dan Allah amman kar kuyi losing hope anyi waya dawani likita daga Maiduguri Teaching Hospital gobe da sassafe ze iso ya dubata inhar da abinda ze iya toh se mu godewa Allah.” Mami dake kuka kamar zata cire ranta tayi k’arfin halin fad’in “likita me kake nufi kenan? har yanzu ban fahimce ka ba ‘yar tawan tana raye ne kokuwa ta mutu?” “Maman Fannah ni kaina banda amsar wannan tambaya zuciyarta na bugawa yana aiki amman kuma bata numfashi, mun samata oxygen munyi komi still ba progress, kwata kwata bata responding to stimuli.” “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un. Malam sun kashe min ‘ya shikenan Fannah ta tafi ta barni, ta barmu Malam” takuma fashewa da wata masifaffiyar kuka Baba na bata hak’uri, shikansa hawaye yake zubdawa shar shar. “Baban Fannah ‘yarku bata gama mutuwa ba tunda tana numfashi, duk me numfashi aikuwa nada rai kenan. Addu’a kawai zaku sata ciki sosai, Allah sa tayi making it through the night in shaa Allah in gobe likitan yazo seya duba ta. Allah bata lafiya ya k’ara maku hak’uri. Excuse mex please.” Nan ya fice. Har k’asa Mami ta sauk’a tana kuka. In ta rasa Fannah ta rasa komai a duniya cikin yaranta uku ba wacce takai Fannah hankali, ‘yar da zaka aiketa sau d’ari a rana barata b’ata rai ba bara kuma tayi fushi ba. ‘yar da kana ce mata bari ta bari kace yi kuma tayi. ‘yar da is ready to sacrfice the last kobo she have just to make her parents happy. Barata iya rayuwa ba Fannah ba. If only zata iya bada ranta asawa Fannah da tayi. Kuka take sosai, abin tausayi, tanayi Baba nayi tabbas shima kap cikin ‘ya‘yan sa babu kamar Fannah. Kalmar son kai ko k’adan Fannah bata sani ba, she can give up her own happiness for others... *©miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [16:09, 12/19/2016] Swtbaby: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 0⃣5⃣ “Malam baran iya shiga ganin Fannah ba, if only zan iya bata raina wallahi zanyi.” “Addu’a zamu mata Maman Aiman kinsan dole ke zaki kwana da ita.” “Yanzu Malam kud’in asibitin fa? Taya zamu biya? Wallahi duk d’an iskan da yama Fannah wannan abu be kyauta ba.” Ta kuma fashewa da kuka hak’uri Baba ke ta bata. “Karki damu da wannan, zan sayar da shanu na in shaa Allah zamu biya bills nata dashi, fatan mu Allah bata lafiya” “Shikenan yanzu dama shanun nan kad’ai muka mallaka, Allah ya isa wallahi.” A sanyaye suka mik’e zuwa d’akin Fannah, Baba na bud’e k’ofa suka hango Fannah kwance kan gado ba alaman nishi a tattare da ita. Da gudu Mami tayi kanta ta tsuguna tare da rik’o hannunta se kuka take zubawa. “Maman Aiman addu’a zamu mata kuka baida amfani barin koma gida in d’ibo muku abubuwan da zaku buk’ata, kiyi hak’uri” ahaka ya fice isarsa keda wuya ya tarar da Afrah se safa da marwah take a parlour tana ganinsa tayo kansa. “Baba ya kun sami Ya Fannah?” Kallon daya mata yasa jikinta yayi sanyi take idanunta suka cike da hawaye “Baba dan Allah meya sami Ya Fannah?” ta tambaya tana kuka. “Afrah da rungumar k’addara aka san musulmi, mun samu Fannah amman yanzu haka tana asibiti.” “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un Baba me kake nufi? Meya samu Ya Fannah?” “Bata da lafiya Afrah, mun... Mun...” Sekuma yayi shiru hawaye na cika a idanunsa sakamakon hakan ya sake tada ma Afrah hankali. Tana kuka tace, “Baba dan Allah ka fad’a min meya samu Ya Afrah.” Zaunar da ita yayi ya bata labarin komai kuka Afrah keyi sosai kamar zata cire ranta sam tace seta bisa asibitin taga yarta. Ba yadda Baba beyi ba dan hanata amman ta dage setaje. Aiman kuwa ta jima da bacci, bayan sun gama had’a abubuwan da zasu buk’ata Baba ya rakata ya tsara mata abin hawa sanda suka b’ace ya dawo ciki. Tafiyar minti 15 ya isar da Afrah asibitin, bayan ta biya sa kud’insa tashigo ciki direct d’akin Fannah ta wuce. Tana bud’o k’ofar taga Mami tsugune gefen Fannah se kuka takeyi take itama wani kukan ya faso mata da gudu taje ta rungumi Mamninsu suna kuka sosai. Sunjima suna abu d’aya sannan Mami ta tambayeta “Afrah me kkeyi anan ina Babanku?” “Mami yana gida na zo ne in tayaki kwana.” “Afrah bekamata kiga yarki a wannan yanayi ba da kin koma gida.” “Haba Mami! Ya Fannah fa yayata ce taya zakice haka?” Nan ta jiyo tana kallon Fannah wacce take kamar gawa. Wani sabon kukan tasoma ta rungumeta, tana kuka “Ya Fannah dan Allah karki mutu ki barmu, Allah ze sak’a miki in shaa Allah.” Da kyar Mami ta lalasheta tayi shiru. Mami ko kayan tean da Afrah ta had’o musu susha tea ma takasa sha hankalinta duk yabi ya tashi. Afrah bata tab’a ganin Maminsu cikin tashin hankali irin wannan ba. Kwana Mami tayi tana nafilfilu tana rok’an Allah haka itama Afrah bawanda yayi bacci cikinsu. **** Washegary da safe misalin k’arfe 8:00AM babban likita daga TH na Maiduguri ya iso. Aikin kusan awa uku akayi kan Fannah sannan likitan yafito. Baba, Mami, Afrah da Aiman dake rik’e a hannun Afrah duk sukayi kansa “likita ya jikin ‘yar tawa?” Cewar Mami jikinta se b’ari yake. “Ku kwantar da hankalinku in shaa Allah ‘yarku zata samu sauk’i tana cikin state of coma ne yanzu within 5-7 days in shaa Allah zata farfad’o.” “Alhamdulillah!” kukeji a wajen. “Likita amman har kwana biyar? Kana nufin barata san inda take ba har nan da tsawon kwana biyar ko bakwai?” “Eh Hajiya, she've been through alot, raping at this tender age ba k’aramin abu bane, tamugun jin jiki, gakuma ruwan daya mata duka again yasa ta kamu da pneaumonia but in shaa Allah inta farfad’o everything will be alright za’a bata magani karku damu.” “Toh likita mungode sosai Allah biya.” “Ba komai” ya fad’i sannan ya fice. A hankali Umma ta soma kuka “Malam yanzu har kwana biyar ko sati ‘yata zatayi batasan inda take ba? Innalillahi wa inna ilaihi raji’un.” “Maman Aiman godiya yakamata muyi tunda Allah yabar mana ita be karb’i abinsa ba, mu cigaba da addu’a in shaa Allah zata samu sauk’i.” *ANAS* _Bawan Allah dan Allah kayi hak’uri kar ka lalata min future, wallahi baran iya baka abinda kake nema ba I'm just 15 dan Allah karka lalata ni kayi hak’uri ka rufa min asiri_ Firgit Anas ya farka daga bacci yana numfashi da k’arfi sosai wanda hakan yasa Shettima tashi shima daga bacci tun jiya yaga yanayin wansa ya canza koda ya tambayesa meh kuwa ce masa yake ba komai, wannan karan ne na farko da Anas ya soma b’oye masa abu. Gadonsa ya bari yaje yasamu Anas tare da dafe kafad’arsa. “Anas lafiya? Ka jima fa bakai mafarkin Ummimi ba, meya faru kuma yau?” “Ba mafarkin Ummimi nayi ba.” cewar Anas yana raba ido. “Mafarkin me kayi toh?” “I don't want to talk about it karka damu its okay.” Anas yayi k’ok’arin calming kansa. “Its not okay Anas, tun jiya nake lura da kai, something is bothering you and you’re keeping it to yourself. Tell me.” “Nace maka ba komai” Anas yayi insisting. A hankali ya mik’e ya wuce bayi. Tun shigarsa bayin ba abinda yakeyi se tunanin mafarkin dayayi akan yarinyar jiya, ko kad’an besamu yaga fuskarta ba a mafarkin. Ruwa ya riga watsa wa a kansa sannan yayi wanka yafito ya shirya kayakinsa da komai dake yau ze tafi Maiduguri, gobe ya wuce Abuja daga can kuma se London. Yana fitowa daga d’akin nasu ya rufo k’ofar yana juyawa sega Amal idanunta sunyi ja “my Angel waya tab’aki?” “Ya Anas wai yau zaka tafi baraka sake dawowa ba se nan da 5 years?” “Waya fad’a miki haka?” Ya fad’a yana wasa da gashin kanta. “Ya Shettima ne kuma wai kana barin gidan nan ze dakeni wai dama tarani yake, Ya Anas dan Allah kar ka tafi” ta rungumesa da tsayinta daidai kunkuminsa. Sama ya d'agata “stop crying kinji Angel? very soon zan dawo kuma duk sanda Shettima ya tab’aki ki d’au wayan Ummie ki kirani I promise in na dawo zamu rufesa a d’aki mumasa dukan tsiya.” “Dagaske Ya Anas? Zamu masa duka?” “Sosai ma bulala zan baki ki zanesa se yayi kuka.” “Yeyyy!” Hugging nasa tayi “I love you Ya Anas.” “I love you too Angel. Sauk’o to muje wajen Abuu.” “O’o ni muje a haka ka d’aukeni for the last time.” “Okay Angel” ya manna mata kiss a goshi sannan yaja akwatinsa suka fice. Suna isa parlour ya sauk’eta tare da gaishe da Abuu sannan Ummie. Breakfast suka ci bayan sungama Abuu ya zaunar da Anas. “Anas kaga karatu zakajeyi ba hutu ba kuma kafi kowa sanin wahalar da mukayi kafin muka samo maka wannan scholarship I'll be very angry inhar baka je kacika mana burinka na zama architecture ba.” “In shaa Allah Abuu” cewar Anas dake kallon kan carpet. “Kasani kuma duk abinda kakeyi Allah na kallonka, kowa yasan ya rayuwar London yake, inbanda iskanci ba abinda sukeyi, ba ruwanka da zuwa beach bale kaje kaga abinda ze hana ka d’aukan karatu. Qur’ani shine guidance naka, karka kuskura kabari rana ya wuce ka baka d’au Qur’ani ka karanta ba. Ba ruwanka da ‘yan mata ko friends na banza. Ba ruwanka da shaye-shaye Anas. Kajini ko bakaji ba?” ya gargad’i Anas tare da rik’e kunnensa. “Naji Abuu na gode in shaa Allah zan kiyaye duk wannan abubuwan daka lisafo, nagode.” “Toh Baba na nikam nasan ko ban ja maka kunne ba kasan what is right and wrong, ban tab’a doubting tarbiyarka ba. Allah baka sa’a ya kareka daga kowani irin sharri Baba na.” Cewar Ummie. “Ameen Ummie nagode.” **** “Amal kukan me ne kuma haka sekace mutuwa yayan naki zeyi? Makaranta fa zasa in shaa Allah ze dawo.” Cewar Ummie tana lalashin Amal dake ta kuka. “Bar shakwab’a de Ummie ke kike biye mata ma ai, tayi kukan jini tagadama ta mutu.” Shettima ya fad’i yana ma Amal dariyan mugunta. Harara ta watsa masa me rai da lafiya “toh nak’i kukan” tasa hannu ta share hawayerta “kaine zaka mutu mugu kawai.” “Ke! Rashin kunya kike min?” Ya mik’a hannu ze finciko ta daga jikin Ummie, hannu Ummie tasa ta make hannun nasa da k’arfi “okay dan Amas yatafi zaka soma cin zalin Amal ko? Toh kasani Anas yace duk sanda ka tab’a ta in kira sa a waya in fad’a masa dan haka ka mayar da hankalinka. Kai kullum kata biye wa ‘yar yarinya duk kabi kasa ta raina ka.” Gwalo Amal tamasa harda sa hannu kan kunnenta. “Ni shikenan Ummie kullum ma wannan maras kunyan zaku na ba wa gaskiya wallahi kicigaba Allah kawo rananda za’a barni dake gidan nan.” ya cize yatsa. “Karki kula sa Amal taho muje mu siya miki sweet ga kud’i nan dayawa Anas ya ajiye miki.” Juyawa tayi tasake ma Shettima gwalo sannan suka fice da Ummie. ***** Da misalin k’arfe 1:00pm Ummie ta kira wayar Anas ringing kad’an yayi ya d’aga “hello Ummie” yafad’a cikin muryarsa me dad’in gaske. “Baba na ya gajiyan hanya?” “Alhamdulillah Ummie tun d’azu muka iso ai, ina gidan chairman ahaka.” “Toh yayi kyau, Babana kaji abinda Abuu ya fad’a maka ai? Nasan kanada hankali kuma kasan abinda ya kamata kar kayi abinda ze haddisa mana matsala kaji ko Babana?” “In shaa Allah Ummie karki damu, ina Angel d’ina?” “Tana parlour tana kallo barin kai mata.” Nan ta mik’e takai wa Amal “ga Ya Anas nasan yanason ku gaisa.” “Ya Anas ina wuni?” “My angel ya kike?” “Lafiya, har kun isa London d’inne?” Murmushi kad’an yayi wanda hakan yasake bayyano da kyansa. “A’a Angel da saura sosai ina Maiduguri ne yanzu se gobe zamu wuce London.” “Okay! Nagane. Ya Anas kaga d’azu Ya Shettima ya nank’washeni akai dan yaga baka nan.” “Shettiman? Bari ki riga irgamin duk mugunta daya miki ina dawowa zamu masa duka.” “Yeyy! Ya Anas I love you ina kallon frozen se anjima.” “Yawwa Angel d’ina bo-bye.” *FANNAH* _6 days later..._ “Mami kukan ya isa mana dan Allah, ki dubi yadda kika rame dan Allah.” Cewar Afrah dake rik’e da Mami itama tana hawaye. “Afrah kiyi hak’uri ba san ra’ayi na bane nima, yau kwanan ‘yar uwarki shida bata san inda take ba taya baranyi kuka ba. Gani nake kamar zata tafi tabarmu. Allah ya isa, haka kawai Fannah bata masa komai ba ya zab’i ya wulak’an ta ta. Allah ze sak’a mata.” “Shhh Mami dan Allah karkiyi magana haka, in shaa Allah Ya Fannah zata farfad’o lets not lose hope Mami.” *** Da azahar misalin k’arfe 1:30PM wani dattijo yashigo cikin asibitin, kallo d’aya za’a masa asan wan Baban su Fannah ne. Zekai shekaru irin 50 a duniya. Baba dake zaune a bakin k’ofar d’akin Fannah ne ya hango wan nasa nan ya mik’e “sannu da zuwa Ya Khaleel.” “Sannu dazuwa fa kace? Ashe iskancin da ‘yarkan tayi kenan shine ka b’oye min kak’i gaya mun, toh Allah ya sanar dani gaskia.” “Haba ya Khaleel ya kake magana haka? Kafi kowa fa sanin halin Fannah ba halinta bane tarayya da d’a na miji.” “Mstww seka gayawa iska ai. Baga erinta ba kullum in na maka magana kan ka hana yarinyan nan ganin samari me kake fad’i? Cemin kake aure zaka mata ba ga erinshi ba, d’aya daga cikin samarukan nata ya mata fyad’e.” Daidai lokacin Ahmad saurayin Fannah da mahaifinsa suka shigowa. “Alhj khaleel me kake cewa?” Cewar mahaifin Ahmad a rud’e. “Ai kajini Alhj Suleiman. ‘yar k’anina Fannah ce, saurayi ya mata fyad’e gata can kwance a gadon asibiti yau kwana shida bata san inda take ba.” “What!?” Alhj Suleiman ya daka tsawa. “Malam Aliyu shin abinda wan ka ke fad’i gaskiya ne? Abinda ya faru kena! kace mana wani ne ya mata fiad’e?” Kwata kwata Baba ya kasa magana ya rasa me yayi ma wan sa Ya Khaleel a duniya ya tsanesa da family’nsa haka. Abin nasa tun daga hassada ya soma tun sanda Fannah ta sauk’e Qur’ani bayan ga d’ansa Farouq dakeda shekaru 22 ko izu biyu be haddace ba. Tun daga lokacin ya d’au tsanan duniya ya d’aura wa Fannah. “Aww bakaji me nace ba kenan?” cewar Ya Khaleel. “Da zaka sake tambayarsa kome yasamu ‘yar iskar ‘yar nasa.” “Abba wallahi nasan komin yaya Fannah bara tayi abinda Alhj Khaleel ke fad’a ba.” “Rufa min baki! Yaro dakai me kasani? Ai gashi baban nata ya kasa k’aryata zancen. Gaskia I'm very disappointed in you Malam Aliyu, na yarda da kai da ‘yarka taya zaku min haka nida d’a na?” “Abba dan Allah kyi hak’uri mujira Baba yayi explaining. Wallahi nasan Fannah yarinya ce me tarbiyya barata aikata abinda ake accusing nata kai ba.” “Amman fa yaron nan baka da hankali.” Cewar Ya khaleel. “Kana nufin kafini san ‘yar tawa ne? In gaskiya tazo dole a fad’e ta.” “A’a barsa Alhj Khaleel I've heard enough. Ahmad taho mu wuce I can’t take this anymore. Gara da Alah ya bayyana mana halinta tun kafin ka aureta.” “Abba dan All-” “Rufa min baki! me zakayi da yarinya me bin maza? Ina kanajin abinda baban nata yace? Saurayi ne ya mata fiad’e ko har yanzu so kake kacemin kanasan auranta?” “Ya isa!” Baba ya daka tsawa. “Kafad’i duk abinda zaka fad’a amman kar ka kuskura kasake kirar ‘yata da sunan me bin maza saboda ko kad’an ba halinta bane. In banda d’anka Ahmad, Fannah bata san wani d’a na miji ba.” Ze k’ara magana Ya Khaleel ya katse sa. “Awww! yanzu kuma so kake kace Ahmad ne ya mata fiad’en kenan?” *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [16:09, 12/19/2016] Swtbaby: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 0⃣6⃣ “Ni ba abinda nake nufi ba kenan, my point is adena kirar ‘yata kariya. Alhj Suleiman kai da d’anka zaku iya tafiya, abincin wani gub’an wani kamar yadda ka k’yamaci Fannah haka wani zeji kamar ya mutu mata. Ahmad Allah had’aka da rabonka, ka kasance masoyin Fannah na hak’ik’aamman there is nothing you can do now dole ka hak’ura kabi umarnin mahaifinka, in zakumin uzuri, I need to see my daughter.” Yana kaiwa nan ya shige d’akin Fannah. Idanun Ahmad take suka kad’a sukayi ja, koda wasa be tab’a tsammanin akoi abinda ze shiga tsakaninsa da Fannah ba, yana santa fiye da yadda yake san kansa. “Abba dan Allah kar muyi haka, wallahi nasan Fannah is innocent.” “Ahmad kaji na rantse maka kasake min maganan wannan kariyan zan tsine maka, ai saisa akace a bincike mutum shiru-shiru. Maza mu wuce gida, Alhj Khaleel nagode sosai Allah bar zumunci.” “Bakomai Alhj Suleiman, ita gaskiya haka take daga k’in jinta kuma se b’ata. Allah rufa mana asiri.” Da fad’in “ameen” Ahmad dake hawaye shida mahaifinsa suka bar asibitin. Suna ficewa ya Khaleel ya b’alle da dariyar mugunta. “Ai dama nace in shaa Allahu ‘yarka barata auri wani ba inba d’ana ba. Kyakkyawar mace me addinin muslinci Farouq ya cancanta kuma ba kowa bace illa Fannah saboda haka tana warkewa zanje in samu Baba (mahaifinsu) in masa magana.” Gida ya zarce yana isa ya soma k’olla ma d’ansa Farouq kira. “Farouq! Farouq! Zo nan” alokacin ya zauna kan wata tabarma bada jimawa ba Farouq d’in yafito da angansa an ga d’an iska wata shegiyar crazy wando ne a jikinsa da singlet. Ba laifi yanada kyau dadai dakuma tsawo. Bayan ya zauna yace, “gani Baba.” Ya Khaleel ya kallesa sannan yace, “d’ana ka kwantar da hankalinka Fannah ta kusan zama taka, Fannah taka ce! Yanzu ana sallamota daga asibiti zan wa kakanka magana.” “Baba dagaske!” Farouq ya tambayi mahaifinsa cike da jin dad’i. “Da dana ce maka seka auri Fannah ka d’au wasa nake maka ne? Ai Fannah taka ce.” “Kai Baba na gode amman da akoi matsala Baba.” “Ina jinka Farouq mecece matsalar yanzu in warkar maka da ita?” “Fannah... Bata so na Baba ko kad’an zan iya irga sau nawa muka tab’a magana da ita, sam bata sona ta tsane ni.” “A da kenan...” Ya khaleel ya fad’a yana murmushin mugunta. “Ban gane a da ba kenan Baba.” Farouq ya fad’a a little bit confused. “A da datake da tabbacin cewa akoi masu santa amman banda yanzu data rasa budurcinta, kap ba na mijin da ze so ta yanzu, ta zamo tamkar k’azantar da akeson a yasar ne yanzu. Ko baka gane ba?” “Sosai na gane Baba na gode.” *** Afrah ce tsaye kan Fannah tana kallonta hawaye suna gangara kan kumatunta a yayinda Baba da Mami suke zaune kan wata kujera, Aiman kuwa an mata shimfid’a a k’asa tana bacci. Hannu Afrah ta mik’a dan ruf’e Fannah mekyau da bargo taga kamar Fannah tad’an motsa. “Barin je in kama ruwa” cewar Mami “ina zuwa yanzu.” Kai Fannah ta kad’a a hankali again. “Ya Fannah! Baba! Mami! Fannah tayi motsi.” Kafin su Mami su k’ariso Fannah ta soma bud’e ido a hankali tagama bud’e idanun nata ta sauk’esu kan family’nta dake tsaye a kanta suna murmushi da zubda hawaye a lokaci d’aya, murmushin tayi k’ok’arin mayar masu da k’yar. “Ya Fannah!” Cewar Afrah “Fannah! ‘yata” cewar Mami. “Mama na!” Cewar Baba. Kallonsu take a hankali cikin wata dashasshiyar murya tace, “Mami, Baba, Afrah.” Dad’a k’aruwa murmushin fuskarsu yayi Baba yace, “Afrah jeki kira nurse kice mata Fannah ta farfad’o.” Bayan minti d’aya Afrah dawata nurse suka shigo d’an dube-dube tayi wa Fannah sannan taceda su Mami “Alhamdulillah condition na ‘yarku is stable. Inda hali a had’a mata tea me kauri tasamu tasha se abata magunanta. Excuse me.” Hugging nata sukayi one-by-one kowa na muranan dawowarta. “Ina Aiman?” ta tambaya a wahalance kusan a tare suka amsata “gata can tana bacci.” “Fannah ya jikin naki?” cewar Mami “Da sau... Argh!” Tasaki k’ara. A rikice Mami tace. “ina ke maki zafi Fannah?” Take idanunta suka cike da hawaye, “k’asa na Mami, zafi.” “Malam ko zaka d’an bamu waje dan Allah” cewar Mami cike da tausaya wa ‘yarta. Bayan Baba yafita Mami ta umarci Afrah ma da tafita ba gardama ta fice. “Fannah kiyi hak’uri dole k’asarki ya miki zafi anji miki ciwo.” Tana kuka tace “Mami ya rabani da budurci na ko? Mami banida martaba yanzu.” Ta fashewa dawata erin matsanancin kuka. “Fannah ‘yata dan Allah kiyi hak’uri kukan nan k’ara miki rashin lafiya zeyi, kiyi hak’uri. Ki d’au wannan k’addara ce Allah ya turo miki.” Cikin kuka tace, “Mami yanzu akoi d’a na mijin da ze yarda ya aureni? Nasan ko Ya Ahmad ze gujeni.” Shiru Mami tai batace komai ba hakan ya sake tabbatar wa Fannah zancenta. “Yama riga ya tafi ko Mami?” Har yanzu Mami batace da ita komi ba se kuka ba sautin da takeyi. “Mami talk to me please, ki fad’a min gaskia.” “Fannah kiyi hak’uri wannan jarabawa ce Allah keson gwada ki, in baki rungumi k’addara ba seki fad’i. Ahmad be k’i ki ba mahaifinsa ne ya tilasta masa se ya rabu dake saboda Kawu Khaleel yace masa saurayin kine ya miki wannan abu.” “Mami amman ai k’arya ne, wallahi bansan shi ba acikin lungu kawai ya tsareni wallahi ban tab’a ganinsa ba inba ranan ba.” “Shhhh! Fannah basekin min bayani ba sanin kanki ne Kawu Khaleel tinba yau ba baya sanki, yayi hakan ne kawai dan ya shiga tsakaninki da Ahmad dan yaga Ahmad nasanki tsakani da Allah.” “Mami me na masa ya tsaneni haka? Mena ma wannan saurayin daya k’wace min martaba ta Mami? Shin na kasance mutumiyar banza ce da duk munanan abubuwa suke faruwa dani?” Hannu Mami tasa ta goge mata hawayen dake gangara kan kumatunta, “ko kad’an habibti, ita duniya haka take mutane masu kind heart su Allah yake jarabta saboda ya gwada nauyin imanin su. Wannan jarabawa ce Fannah you have to be strong.” ***** *ANAS* D’aki ne babba da gadaje guda uku ciki, haka wardrobe ma, sannan da bathroom aciki. A d’aya daga cikin gadajen Anas ke kwance akai da earpiece a kunnensa wanda ke had’e da wata sabuwar Iphone 6s ajiye kan cikinsa. Sanye yake da ¾ wando da vest bak’a ya zura wa ceiling ido se tunani yake. Bada jimawa ba wasu samaruka guda biyu suka shigo wanda suke nan sa’anin Anas, da angansu anga ‘yan hutu. Gado d’add’aya suka d’auka suka kwanta kai har alokacin Anas besan da shigowarsu ba. Pillow d’ayan ya wulla masa a firgice ya mik’e ya zauna ganin su ne yasa ya sauk’e ajiyar zuciya. “Mehn! Yaushe kuka shigo bansani ba.” “Well kayi nisa a tunani taya zakayi noticing shigowarmu?” cewar na k’arshen. “Waima tunanin me kake haka? Kullum fa cikin tunani kake ko ka bar mata da ‘ya‘ya ne acan gda 9ja?” suka k’yalk’yale da dariya illa Anas daya tsaya yana kallonsu. “Musty waikam meke damun Anas ne?” cewar d’ayan. “Ji Abdul de da wata magana budurwarsa ce ni da zan sani?” “Oh oh no please banda maganan budurwa anan” Anas ya fad’a in an angry tone. “Wai Anas kai kullum haka kake ne? Ban tab’a ganin kayi dariya ba wallahi, whats wrong with you? And anytime aka kawo maganan girlfriend you seem so moody.” Cewar Abdoul. “Nima de, abin have been bothering me.” Hannu yasa yaja d’aya daga cikin bedside drawer’n gadonsa tare da ciro wani syrup ya wulla wa Anas karap ya cafke. “Meh wannan kuma?” “Wannan!” yad’an murmusa “lets say anti-problem kokuma problem reliever.” Shida Abdoul suka kwashe da dariya. Kallaon syrup d’in Anas yayi sannan ya ajiye kan bedside drawer’n nasa “no thanks barin sha ba.” “Chill bro!” cewar Musty. “It'll ease all your problems just give it a try.” Haka suka ta cika masa baki kan in yasha ze manta yanada problem ko d’aya akansa seya d’auka ze sha seya tuna wa’azin da Abuu yamasa amman kuma problems sun masa yawa right now gana Ummimi gakuma na yarinyar daya yi raping. Rufa ido kawai yayi daga k’arshe yasa kwalban syrup d’in a baki. “Dude (maza) karka shanye duk-” be k’are maganar ba Anas ya kauda kwalban syrup d’in daga bakinsa sanda ya kwankwad’e tas. Fuska ya yamutsa trying to adjust and in just 3 minutes Anas ya fad’a bacci, baccin daya jima beyi ba in a lifetime. _7 hours later_ Daidai 8:30PM Anas ya tashi, ko sallan la’asar, maghrib da Isha beyi ba duk yini yayi yana bacci. “Holy shit!” Ya fad’i. Sede kuma kap ya nemi problems nasa ya rasa, da yayi niyan bare sake shan syrup d’inba amman dan yadda ya masa aiki he can’t resist it. Daidai ya mik’e ze shiga toilet Musty da Abdoul suka shigo da angansu anga wad’anda suka dawo daga party, dan aikinsu kenan. “Ya dude har ka tashi ne?” Musty ya tambayi Anas yana k’ok’arin zama. “How did you like the syrub? Your problems will all be gone for good two days and after that seka nema ka sake sha, continiously” Abdoul ya ma Anas bayani tare da fad’awa kan gadonsa da baya. “Great!” Anas ya ce, “I can’t remember any of my problems now saidai nata bacci ko sallan la’asar banyi ba.” Tsuka Abdoul yaja “yanzu dan kawai yau ka rasa sallolin nan shine wani abu? Kaifa Anas kanada case, wannan blue eyes naka basu taimake ba. Nifa the first time I saw you nad’au American ne kai to seme dan ka share sallolin yau?” “Tell him bro” cewar Musty. D’an murmushi Anas yayi lallai duk iskancin mutum dubu sun fisa, can a Bama sune ‘yan iskan gari nan kuwa a tafin hannun su Abdoul yake be sauraresu ba yashige toilet yayi alwala yafito ya rama sallolinsa. Da misalin k’arfe 11:30PM su Musty suka kuma yin wanka suka yi shiri tsaf a yayinda Anas keyin zanen project da aka basu a school. Da suka zo fitane suka juya suka kallesa tare da kad’a kai. “Anas wai kai ko kad’an baraka gwada zuwa clubbing d’innan bane? Wallahi its fun, more fun than wannan jakin project da kakeyi na 5 marks kacal.” Cewar Musty ransa a b’ace. “No kuje kawai, I have to get this done, maybe next time.” Anas ya sanar dasu yana d’an murmushi. “Dude listen to him, ko na yau ne kazo muje club d’innan.” Cewar Abdoul. Kai kawai ya kad’a masu bayan sun fice yayi rounding up abinda yakeyi ya kira Ummie bayan sun gaisa yasa ta mik’a ma Angel nasa suka ta hira abinsu. Anas na mutuwan san Amal badan komai ba dan abinda Ummimi ta mata. Ace yarinya kwanan ta d’aya a duniya amman dan rashin imani tasa a dawo da ita gida ko shayar da ita batayi ba. _2 days later_ Da misalin k’arfe 12:30PM Anas na kishingid’e kan wata couch (kujera me fad’i da akan iya bacci akai) yana bacci. Ya soma mafarki; _“Ummimi dan Allah karki tafi kiyi hak’uri indan plates dana fasa ne I promise baran sake ba. Ummimi I am sorry dan Allah karki tafi. Abuu ka hana Ummimi tafiya dan Allah kace mata I will be a good boy from now on.”_ _“Yanzu Aysha bara kiji tausayin yaranki ki hak’ura ki zauna dasu ba. Kalli yadda suke kuka fa?_ _“Mstww wannan kuma ku ya shafa nagaji da zama cikin talaucin nan, ace kullum se atashi ba’a san me za’a karya dashi ba gaskia nagaji daman tun farko sanda Abba na yace kar in aureka matsiyaci ne kai amman nak’i sauraronsa. Ga can miji Allah yamin har k’asar waje ze kaini saboda haka ban ga abinda zesa in cigaba da zama a wannan gidan ba.” Jakarta ta ja ta soma tafiya da sauri naje na kama k’afarta ina kuka ina rok’arta wani wawan ball tayi dani da k’afa sanda na ji ciwo a elbow na...”_ “UMMIMI!” Anas ya kira da k’arfi a yayinda ya farka daga baccin dayakeyi duk zufa yakeyi se nishi yake da k’arfi ganin mafarki yake yasa hankalinsa yad’an kwanta. Wani erin mahaukacin bacci yakeji saboda jiya kwana sukayi a studio amman saboda duk sanda ya rufe idansa mafarkin Ummimi yake yasa ya kasa baccin abu d’aya ne yasan inyasha ze gusar masa da problems nasa which is syrup na problem reliever (giya) da Abdoul ya basa ranan. Kash! Saidai basu gida sun fita yawo gashi bacci yakeji. Gwada jirarsu yayi na ‘yan mintuna ganin basu dawo ba yasa ya kira sa a waya kai tsaye ya tambayesa ina yake ajiye syrup daya basa ranan yana san sake sha. Dad’i sosai Abdoul yaji finally Anas is ready to change, bayanin ina yake ajiye wa ya masa yakuma tabbatar masa in zasu dawo gida ze sake siyowa tunda wanda ya rage kad’an ne. Exactly inda Abdoul yamasa kwatance yasamu syrup d’in bud’e sabon kwalb’a yayi yakafa a baki sanda yashanye tas, ko cikakken minti biyu beyi ba yasoma jin bacci me nauyin gaske tsalle kawai yayi ya fad’a kan gadonsa yasoma wani erin mahaukacin bacci me uban nauyin gaske *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [16:09, 12/19/2016] Swtbaby: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 0⃣7⃣ *FANNAH* _3 days later..._ Kwanan Fannah uku a asibiti tasamu k’arfin jiki aka sallamesu, ayau suke shirin dawowa gida, Alhamdulillah jikin nata da sauk’i sosai saboda anti-biotics datake sha masu k’arfi ne sosai. Baba ya sayarda shanunsa da shi ya samu ya biya kud’in asibitin ta da kuma na magunanta. Daidai sun sauk’o daga keke na pep kenan se ga irin almajiran unguwan nan sunzo sun tsaya gabansu. “Fannah! Dama ashe ke d’in kariya ce me bin maza, sekitayin abu kamar ‘yar malam saliha to Allah ya tona miki asiri tunda saurayi yayi miki ciki.” Hannu Mami ta d’aga ta wanke sa da mari. “In na sake jin wannan munanan kalamu daga bakinka kaji na rantse seka kwana a asibiti, bakai kad’ai ba dukanku nan. Fannah ba kariya bace abinda ya sametan nan k’addara ce. Maza ku fice min daga kallo.” Baya sukayi kad’an sannan suka soma wak’a “kariya! Kariya! Fannah kariya Fannah kariya!” Hannun Fannah kawai Mami taja suka shiga ciki a yayinda Baba ya koresu. Kuka Fannah keyi sosai. “Yanzu shikenan Mami kallon kariya za’a na mun? Shikenan rayuwata ta lalace Mami.” “Shhh karkiyi magana haka, karki saurare wad’ancan almajiran basu masan me suke fad’i ba.” Hugging nata tayi har sanda Fannah tayi shiru. Da yammacin ranar around k’arfe 4:45PM Ya Khaleel da d’ansa Farouq suka shigo gidansu Fannah. Mami da Afrah suna had’a girkin dare suka masu sannu da zuwa, ba abinda Afrah ke masu se harara. “Ke Afrah jeki kira min mahaifinku dakuma ‘yar ku kariyan can.” cewar Ya Khaleel. “Kawu Khaleel bamuda kariya a gidan nan.” Ta fad’a stubbornly. “Ke ni keke gaya wa magana? Iyye?” “Kawu kayi hak’uri Afrah kibasa hak’uri kije ki ma Babanku da Fannah magana.” A sanyaye ta mik’e taje ta kira Baba sannan takira Fannah a tare suka fito. Fuskar Baba a tamk’e ya zauna kan tabarman da Ya Khaleel da d’ansa ke kai ba tare da ya musu magana ba. “Ina wuni kawu?” Gaisuwar Fannah. “Yawwa sannu an sallamoki kenan. Se a kiyaye aukuwan na gaba kafin wani saurayin yasake fiad’e ki.” Har tsakiyan kanta tajiyo wannan kalamai ba ita kad’ai harsu Baba da Mami da Afrah. “Ya Khaleel in kasan batun daya kawo ka gidana dan kaci zarafin ‘yata ne dan Allah kayi hak’uri na had’aka da Allah ku tashi ku tafi.” “Ba seka koremu ba yanzu zamu tafi. Magana d’aya biyu na zoyi nan saboda haka nakeson ku bud’e kunnuwanku ku saurareni. Kunfi kowa sanin yadda ake k’yamatan kariya a gari, ba uban da ze so d’ansa ya auri macen da batada budurci. Fannah kuwa ‘yata ce dukda abin kunyan da ta mana ina san ta saboda haka zan bata wa d’a na Farouq.” “What!?” Baba yayi exclaiming. “Bari na gama mana k’ani na. Na riga nayi wa Baba magana kuma ya goyi bayan zancen d’ari bisa d’ari bawai nazo nan bane in baku choices saboda bakuda choice inbanda ku yarda mu rufa wa kariyarku asiri dan na tabbata kap garin nan bame san aurenta. Kinji ai Fannah? Ga Farouq nan mijinki, kina k’are secondary ze rufa miki asiri ya aureki zaki iya gode masa saboda wannan jahadi yayi. Auren kariya ba wasa bane.” D’ago jajyen idanunta tayi ta azasu kan Farouq dake ta mata murmushi. Hawaye se gangara suke kan kumatunta, kuke take sosai. Tasani a yanzu kam kamar yadda Kawu ya fad’i ba na mijin da zeso aurenta saboda ta rasa budurcinta martabatar ta, amman duk da haka gomma ta mutu batai aure ba data auri Farouq. Farouq baida tarbiyya ko kad’an d’an iska ne ba aikinsa se bin mata Allah kad’ai yasani ko baida cutar k’anjamau ma. Ba yadda za’ayi ta auresa. “Kawu dan Allah kayi hak’uri ni baran auri Ya Farouq ba, dan Allah ka rufa min asiri.” “Ji shashasha dabadan Farouq nada imani bama jinki ze yarda ya aureki ne? Ajinki a kariyan da kike yanzu zaki samu na miji kamar Farouq yace ze aureki ne? Inba mahaukaci ba wallahi ba na mijin de so ya aureki gara ma tun wuri kinsan ina ke miki ciwo” “Enough Ya Khaleel!” Cewar Baba a fusace. “ ‘yata barata auri wannan d’an iskan ba. Mungode da alfarman da kuka bamu amman bamuso da in aura wa ‘yata d’an iska kaman Farouq na gommaci kartayi aure a duniya. Yaro ko gaishe dana gaba dashi be iya ba. Ku tashi kubarmin gida zanje in samu Baba in masa magana yaja da baya da wannan zance. Fannah bata san Farouq saboda haka barin tilasta mata ba.” “Aww haka kace kenan? Yanzu har zaka bud’e baki ka kira d’a na Farouq d’an iska? Kariyarka kuma fa? ai nakega sede ace mata ‘yar guguwa, aure tsakanin Fannah da Farouq kuma consider it done bari ta k’are shirmen secondaryn nan kuga ikon Allah. Wawiya ana taimaka miki kina wawanci mschww Farouq tashi mu tafi da Allah.” Suna ficewa Fannah ta ruga d’aki da gudu ta baje kan katifar ta tana kukan cire rai. Afrah ce tabiyo bayanta itama kukan take tabbas Fannah tana cikin tsaka me wuya duk wanda ya aikata mata ta’addancin can ya cuce rayuwarta har a bada. Tun ba yau ba Fannah ta tsani Farouq taya za’ace shi zata aura? Kasheta akeson yayi? “Yi hak’uri Ya Fannah dan Allah kibar kukan nan in shaa Allah baraki auri Ya Farouq ba.” D’ago jajayen idanunta tayi “Afrah shikenan ni haka rayuwata zata k’are cikin k’unci da bak’in ciki? Mesa se ni Afrah? Mena tab’ayi da ba kyau to deserve all this? Duk abinda addini na yace inyi inayi wanda kuwa ya haramta ina k’ok’arin nisantar kaina daga aikatasu. Mesa seni wancan saurayin zeyi raping? Mena masa Afrah? Mesa seni za’a ce zan auri Ya Farouq kinfi kowa sanin halinsa. Kullum yana nan a bayan gari yana kwanciya da mata, Afrah dan Allah ki taimaka min.” Ta kuma fashewa cikin matsanancin kuka. Itama Afrar kuka take ta rungumi yarta tana bata hak’uri. **** “Malam dan Allah kayi wani abu karka bari Kawu ya cimma burinsa na aura wa Fannah aure da Farouq kafi kowa sanin halin Farouq so nawa ake kamasa a bayan gari? Dan Allah kaji k’an ‘yarmu Fannah. Ko kad’an she’s not to blame for what happened to her fiad’e aka mata munyi iya binciken da zamu iya mun kasa samun waye ya mata wannan d’anyen aikin.” Ta fashe da kuka. “Maman Aiman in shaa Allah barin bar Fannah ta auri Farouq ba. Yanzun nan zanje in samu Baba in masa magana kishiga ciki kibata hak’uri ki kwantar mata da hankali dan Allah. Ni na wuce...” **** “Ina wuni Baba?” Gaisuwar Malam Aliyu Babansu Fannah ga mahaifinsa da Ya Khaleel. “Lafya Aliyu, ya jikin Fannan?” “Da sauk’i Baba.” Ya amsa yana kallon wansa Khaleel da d’ansa dasuke zaune a gefen mahaifin nasu. “Nasan maganan daya kawo ka Aliyu saboda wan ka Khaleel yamin bayanin komi yanzu. Kasani wan ka bare tab’a maka abinda ze cutar dakai ko iyalinka ba. Kafi kowa sanin halin da ‘yarka tashiga kallon kariya ake mata agari me bin maza-” Malam Aliyu katse mahaifin nasu “amman Baba ai duk munsan ba haka asalin abar take ba, fiad’e aka mata.” “It still will not change anything Aliyu, in mu mun yarda da hakan mutane fa? Baramu iya fahimtar dasu ba. Kap garin nan ba mahaifin da ze b’ar d’ansa ya auri wacce batada budurcinta tattare da ita kasani Aliyu. Allah ya kawo mana sauk’i gida ga wan ka nan Khaleel he is ready ya rufa wa ‘yarka asiri ya d’au d’ansa ya aura ma ‘yarka dukda ba cikakkiyar mace take ba yanzu amman har ka bud’a baki kace bakaso? Ina zaka zo ka kai ‘yar taka?” “Baba in shaa Allah, Allah ze kawo mata miji wanda ze sota a yadda take.” “Har tsawon yaushe kuma zaka tsaya kana jiran wannan rana da bakasan ranan zuwanta ba? Iyye Aliyu? Bana sake jin wani zance, Fannah zata auri Farouq wannan shine san da muke mata bamusan tak’are rayuwarta batayi aure ba.” “Baba dan Allah kayi hak-” Baba ya katse sa. “Aliyu wannan shine karo na farko da kake k’ok’arin bijire min, kar muyi haka da kai. Farouq.” ya waiwayo da kallonsa kan Farouq “Na’am Baba.” cewar farouq. “Kanason Fannah zaka aureta koda bata da budurcinta a tattare da ita?” “Eh Baba ina santa k’anwa tace koda duniya sun k’ita ni baran k’ita ba.” “Masha Allah” Baba yace. “Kaikuma fa Khaleel ka yarda d’anka ya auri macen da tarasa budurcinta?” “Na yarda Baba” cewar ya Khaleel. “Fannah ‘yata ce matuk’an ina raye zanyi duk iya abinda zan iya dan in kula da ita in rufa mata asiri.” “Toh masha Allah kadeji Aliyu. In nine kai godiya zanyi wa Khaleel da Farouq.” “Baba amman Fannah batasan Farouq, bata tab’a sansa ba, taya zamu tilasta mata auren wanda bata so.” Cewar Malam Aliyu. “Wannan kuma ba me wuya bane, in suka soma ganin junansu a hankali zasu shak’u. Allah dad’a had’a kawukan ku.” “Ameen” Ya Khaleel ya amsa banda Malam Aliyu dake ji kamar yayi kuka. **** “Sannu da dawowa Malam” cewar Mami tana k’ok’arin shimfid’a masu tabarma. Bayan sun zauna take tambayarsa ya had’uwan nasu ya gudana. Kai ya kad’a a hankali take jikinta yayi sanyi. “Maman Aiman Ya Khaleel ya riga ya saye Baba nuna masa yayi intensions nasa are clean tsakani da Allah yakeson ya aura wa Fannah Farouq saboda tsantsan tausayi.” “Malam amman ai duk munsan badan haka bane.” Mami ta katse Baba. “Tun ba yau ba idanun Kawu suke kan Fannah shikansa yasan tana da tarbiyya mekyau da hankali so yake ya aura wa Farouq Fannah saboda ta giara masa d’a ita kuma tasha wahala in the process.” “Ba k’arya cikin magananki Maman Aiman ni kaina abin nan ya dameni bansan ya zanyi ba, tausayi Fannah take ban matuk’a yarinya me hankali ace arasa ma wa za’a d’aura wa k’addara erin wannan se Fannah.” yaja numfashi. “Uhn uhn Malam kayi istigifaar kar kayi sab’o. Wannan Allah kad’ai yasan mesa ya d’aura wannan mumunar k’addara kan Fannah bekamata muyi ma Allah shisshigi ba.” “Hakane Maman Aiman Astaghfurullah.” “Yanzu Malam shikenan sede mu zuba ido muna ganin ‘yarmu zata auri wannan d’an iska? Ba abinda zamu iya mata? Innalillahi!” “Da akoi abinda zan iya da nayi Maman Aiman banasan Fannah ta auri Farouq ko kad’an. Ran Baba ya b’aci ya dage se Fannah ta auri Farouq inhar na hana aikuwan wannan aure, zamu iya samun sab’ani da mahaifina.” Fannah dake lab’e ajikin bango tana sauraronsu ba abinda takeyi se hawaye. Daidai lokacin wani yaro yashigo gidan bayan ya gaisheda Mami da Baba yace “wai Fannah tafito inji Farouq.” “Barata fito ba” cewar Baba a fusace. “Kace masa barata fito ba inji mahaifinta.” Nan Fannah dake lab’e tafito “kace masa ina zuwa.” “Fannah!” Mami da Baba suka kira a lokaci d’aya. Tana kuka tana maganar, “Baba naji duk abinda kuka fad’a barinso saboda ni kasamu matsala da Baba ba. Muyi hak’uri mu rungumi k’addara fatarmu Allah sa hakan shi yafi alkheri, Allah sa auren Farouq ba sharri bane a gareni, addu’an da nake so kumin kenan. Barinje kirarsa kar yaje yasamu Baba ya fad’a masa wani abu daban yajawo maka matsala.” Tana kaiwa nan ta fice. Kuka me k’arfi Mami ta fashe da shikansa Baba sanda ya zubda hawaye, babu kamar Fannah, yarinya me hak’uri da hankali dole yasan abinda zeyi ya hana aukuwan wannan aure. Tana fitowa taga Farouq zaune kan benchin da take zama kullum da Ahmad nata take hawaye ya ciko mata a ido. “To ke kuwa Fannah haka ake hira? Haka kika sabayi ne in samarukan ki sunzo wajen ki? Taho nan mu zauna mana.” Kafin tace meh Farouq ya taso ya cafke hannunta da sauri ta waske hannun nata daga rik’onsa. Tana kallonsa da jajayen idanunta. “Meh haka kuma? Yau na miji ya soma rik’e hannunki ne? Kinga nifa ki sake jikinki dani tunda nasan ciki nasan waje ba sekin tsaya kina proving min innocence ba.” Hannun nata yasake rikowa da k’arfi sannan ya aza d’ayan hannun sa kan fuskarta yana shafawa. “Ji laushin jiki wai a haka ma kinbar samaruka suna tab’awa kenan.” K’ok’arin k’watan kanta take amman ta kasa se hawaye take yi “Farouq kasake ni bana so, kadena tab’ani.” K’in saketa yayi “meh aciki dan na tab’a mata ta ko kin manta a matsayin mijinki nake yanzu.” Matso da fuskarsa yayi sosai kusa da nata. Numfashinsu yana had’uwa. Kafin ya hankara Fannah ta tsinke sa da mari wanda besan sanda ya saketa ba. Hawaye take sosai “karka kuskura ka sake tab’ani in kai d’an iska ne toh ni ba ‘yar iska bace, in ka saba tab’a mata anyhow ni ba d’aya daga cikin ‘yan matan da kasaba tab’awa bane.” “Dallah can kariya kawai, keda kike bin maza kowa ya sani, zaki wani zo kina min zak’in baki. Kuma barikiji in fad’a miki duk sanda kika kuskura kika sake marina wallahi kinji na rantse sekin sake kwana a asibiti. Humm!” ya sakar da wata shu’umar murmushi bari a aura min ke zaki yaba wa aya zak’inta. Se gobe ko baby, ki kula min da kanki please karki sake bin wani har abu yakuma shiga tsakaninku nasan you are itching to be with a guy.” *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [16:09, 12/19/2016] Swtbaby: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 0⃣9⃣ *United Kingdom, London* *ANAS* _shima bayan shekara d’aya..._ Acikin babban Beach dake waje da London, Anas ne mik’e kan wata doguwar kujera da blue sunglasses a fuskarsa kwata kwata short nicker ne kad’ai ajikinsa seda headphone dake kansa wanda ya had’a da wayarsa yana nin cool music. Kallon sama yake yayi nisa cikin tunani. Bottled wata aka wulla masa a firgice ya mik’e ganin Musty ne yasa yayi murmushi wanda ya bayyano da fararen hak’waransa. “Kai! Abdoul where are you? Yau Anas yayi murmushi harda ciro hak’wara. Tell me why do you seem so happy?” Murmushin ya sake, “my dreams are coming true one-by-one.” cewar Anas. “Wani dream kenan Anas?” Musty ya tambaya. “Humm!” yakuma murmusawa ta gefen da dimple nasa yake. “Ni dreams d’ina guda uku ne kacal a duniyan nan.” Musty ya giara zama “ina jinka!” “Kaga na farko to be a billonaire not a millonaire but a billonaire. After that kaga in nayi kud’i I can toy with women hearts, saboda one thing I've learnt in life is ba abinda mata sukeso fiye da kud’i a duniya, zanyi amfani da wannan damar in saye zuk’atarsu dashi, akan kud’i they are ready to sacrifice everything I mean everything harta family'nsu, kaga ko in nayi kud’i nasan ba macen da zata k’i ni ko akoi?” Ya tsaya ya tambayi Musty. Musty dake jin dad’in wannan labari yace, “ai ko a yanzun ka ma ba macen da zata k’ika Anas you've got the looks and the blue eyes also.” Murmushi sukayi dukansu “ehemm. Ina jinka...” “Yess! As I was telling you, inason inyi wasa da zuqatan ‘yan mata a k’alla 100-200. So nake na karya musu zuqatansu ta yadda barasu sake san kawo na miji cikin rayuwarsu ba, so nake su d’and’ana how it feels to be left alone.” Kai Musty giad’a a hankali alaman yana gane abinda Anas ke nufi “so in ka karya masu zuqatan nasu what will you benefit from it?” Daidai lokacin Abdoul yazo ya zauna dawata American babe kan cinyarsa tasha bikini (pant and bra) “Hi Fauzy!” Tace da Anas sunan da ake kiransa dashi a can London kenan kasancewar su turawa sun saba da kiran mutum da family name nasa (ANAS IBRAHIM FAUZY) Ba tare da ya kalleta ba yace “hey.” Abdoul ya d’ibi k’asa me laushi dake beach d’in ya watsa wa Anas. “Budurwar tawa ma seka ja mata aji ne? Kaifa Anas daban kake I keep on telling you.” “Abdoul kaga magana muke da mazan nan kuma kallon wannan me farin gashin kusa dani amai yake sani so please ka koreta kokuma ku tafi tare.” Cewar Anas batare da ya nuna damuwa ba. “Allah...!” Abdoul ya fad’i cike da mamaki wai ace baturiya ma bata burge Anas ba to wace zata burge sa!? Dariya sosai Musty ya fashe da ba k’arya maganan Anas ya sasa dariya. Baturiyar ce ta tsargu danko ba jin yarensu take ba. “Hey Auwal (family name na Musty) whats funny why you laughing?” Dariyan yake har yanzu “ohh Emily its nothing don’t worry.” Bayanta Abdoul ya shafa “excuse us babe I'll be right back.” Kiss ta manna masa a cheek sannan ta tashi ta fice. Fuska Anas ya yamutsa a k’yamance yana mamakin Abdoul wai har baturiya yake bari tana masa kiss. “Seka sake fuskarka ai tunda na miji da na miji kaga suna kiss ba.” Cewar Abdoul a little bit pissed off. Murmushi kad’an Anas yayi “LOL mamaki kawai kuke bani, I can’t waste my time on girls. They aiint worth it” “Aini Anas da ban sanka ba senace gay ne kai.” Cewar Abdoul “anyways what are you two discussing about da kuka sa na kora Emily.” “Labari Anas ke bani” cewar Musty yana jin dad’i. “Ehem ina jinka continue.” Komawa yayi ya jinginu jikin kujerar sa yana kallon sama sannan ya cigaba “kace what will I benefit in nayi breaking hearts na mata?” Musty ya giad’a kai dukda ba kallonsa Anas yake ba. “I will benfit everything, zan ramawa Abuu abinda Ummimi ta masa, dukda ba direct kan Ummimin zan d’au revenge d’inba atleast ‘yan uwan ta mata zasuji jiki tunda ciwon ‘ya mace na ‘ya mace ce.” Cikin rashin fahimta Abdoul yace, “wait wait nade san waye Abuu mahaifinka ba? what of Ummimi? Wace ita? As far as am concerned Ummie nasani mamanka har kana bamu waya muna gaisawa.” Numfashi Anas yaja “well apart from my family you guys are the first people da zan bawa wannan labari so listen closely after na baku labarin seku fad’a min ko inada laifi in nace mata are evil creatures da be kamata a tausaya masu ba.” _[Abuu kamar yadda kuka sani mahaifi na ne kanurin Bama ne dake jihar Borno. Ummimi kuwa mahaifiya tace unfortunately, asalin shuwa arab ce daga Maiduguri. Mu uku ne gun iyayenmu nine babba I'm 19 years old, followed by my brother Shettima shikuma he is 17½(sha bakwai da rabi) yanzu. Shekara 1½ (d’aya da rabi) ne tsakanin mu sekuma little sister’nmu my angel Amal she's just 9 years old.]_ _[Base on yadda Abuu yabani labari auren soyayya shida Ummimi sukayi. As you guys know scholarship nasamu nazo nan school d’in not like you guys da iyayenku suke biya muku da kansu. Abuu bashida wani arzikin azo agani, yanada arziki ne dadai na rufin asiri a yanzu haka in za’a kira masu arzikin garinmu Bama nasan definately za’a sa Abuu amman dekam bade da kafin sui aure da Ummimi ba. Shi da kansa yake bamu labarin irin rayuwar talaucin da sukayi shida Ummimi kafin a haifemu harkuma da aka haifemu so dayawa ana tashi a gidanmu ba’a sanin me za’a ci.]_ “You guys must be wondering ya akayi Ummimi shuwa arab da uban san kud’insu ta auri talaka kamar Abuu na ko?” Ya juya ya kalli abokansa. Kai suka giad’a a tare murmushi ya saki kad’an “well you don’t have to.” _[Alokacin da Abuu yaje Maiduguri yin diploma ne ya had’u da Ummimi tana sayar da abinci a school nasu a lokacin iyayenta sun kasance talaka sosai amman kunsan shuwa arabs koda su talaka ne se masu kud’i sukeso unlike Ummimi back then, dukda tasan Abuu baida kud’i makaranta yake hakan be hanata falling masa ba kamar yadda shima ya juma da falling mata dan kyan ta dakuma hali, sosai Ummimi kyakkyawa ce kap mu yaranta kamanninta muka dauka sede nafi kama da ita fiye da Shettima da Amal wanda har yau in na tuna da haka se inji kamar inje inyi plastic surgery in canza kamanni na sam banasan abinda ze sa ina tunawa da ita but anytime I look at myself in the mirror ita kawai nake gani...]_ Musty da Abdoul da suke duhu sukace “ban gane ba” a tare. “Mesa ka tsani mahaifiyarka haka Anas?” Cewar Musty. “Shin yanzu bata gidanku ne?” Abdoul ya tambaya. “Zakaji reason dayasa na tsaneta Musty, bata gidanmu Abdoul Allah kad’ai yasan ko tana nan aduniya ko lahira.” “Babbar magana!” cewar Abdoul “kanada picture’nta inasan ganin ta.” Hannu Anas ya mik’a ya d’aga wallet nasa daga kan wata ‘yar table ya bud’o sannan ya ciro wata hoto “wannan family picture’nmu ne Abuu, Ummimi se nida Shettima time d’in ba m’a haifi Angel ba. Sede bara ku gane fuakarta sosai ba saboda na dirje da biro.” Nan ya mik’a wa Abdoul sosai kam ya dirje fuskar Ummimi a hoton se ansa ido sosai za’a d’an ga kutsirin fuskarta amman ko a hakan ma za’a gano kamanninta da yaranta musamman ma da Anas kamar yadda ya fad’i bayan Abdoul yagama gani ya mik’a wa Musty, shima daya gani yayi returning wa Anas, amsa yayi tare da mayar wa cikin wallet nasa sannan ya cigaba; _[Sun yi shekaru biyu suna soyayya batare da sanin iyayensu ba lokacin da Abuu yagama polythecnic ne ya sanarda da iyayensa kan yasamu mata kuma yanasan ya aura dukda cewar ba aiki yake dashi ba. Kowa murna ya tayasa seda akaji batun Shuwa Arab ze aura ne hankalin kowa ya tashi gudun heartbreak da suke masa dan sunsan for sure in iyayen Ummimi sukayi learning truth about status na Abuu barasu yarda suba d’ansu wa talaka ba sunfi san wanda ze kawo masu gwala gwale yakai su Hajji da umara.]_ _[As expected da Ummimi tayi introducing Abuu wa iyayenta sam sukace ‘yarsu barta auri talaka ba suka masa kaca-kaca sannan suka koresa. Amman dan erin soyayyan da Ummimi kema Abuu yasa ta bijirewa iyayenta tace ita sam inba Abuu ba zata kashe kanta kuma she was serious duk suka tsorata ba yadda suka iya dolensu suka yarda mata saboda ita kad’ai ce ‘ya a garesu. A munafirce mahaifinta ya tura ‘yan uwansa suka tsare Abuu a hanya suka masa tsinannen dukar mutuwa basu barsa ba sanda suka ga baya numfashi jinyan wata d’aya Abuu yayi kafin ya samu sauk’i alokacin Ummimi ta tada borin inba a aura mata Abuu ba zata fad’a rijiya dole aka musu aure iyayenta wane bak’in ciki ya kashe su]_ _[Bama ta biyo Abuu aka basu BQ a family house nasu Abuu. Aiki Abuu yashiga nema dan earning living and to make his beautiful wife happy but kunsan yadda k’asarmu take sam be samu aiki ba haka ya soma noma, safe, rana, yamma, dare. Duk sanda yayi harvesting shuk’ansa once in a year yakan kai maiduguri ya siyar a wannan lokacin ne yake samun kud’i ya ma Ummimi siyayya and duk abinda ya kawo mata tana appreciating. Bayan shekara d’aya da aurensu aka haifeni Abuu yace ni ko ragon suna ba’a min ba sanda nayi wata uku tukuna. Sam basu ji dad’in haifan Shettima da akayi bayan shekara d’aya da rabi da haifa na ba dukda cewar kowani d’a da arzikinsa amman talaucin nasu yayi over. So dayawa ana wayen gari ba’a san me zamuci ba. Mahaifin Abuu ke turo mana abincin dazamu ciki.]_ _[Daga bayan Shettima kuwa Ummimi bata sake samun ciki ba. Shekarana goma a duniya lokacin Ummimi tasoma staying late at night seta fita tun safe bata dawowa se dare abin ba k’aramin damun Abuu yake ba. Da ya d’anyi bincike kuwa se aka gano wani Alhaji ne daga Yola take had’uwa dashi. Attajiri ne sosai yanada kud’i Abuu yace kullum cikin canza mota yake. Yana ganin Ummimi kuwa ta masa kyau ya fara nemanta ita kuma saboda cin amana tak’i fad’a masa tanada aure. Soyayya sosai suka fara sam Ummimi tadena kula damu kullum cikin dukan mu take kamar ba yaran cikin data haifa ba.]_ _[Koba abin duka ba seta bugemu musamman ma a weekends lokacin da wannan Alhajin nata ya koma Yola ba me bata kud’i. Ranar lahadi da sassafe baran tab’a mantawa da wannan rana ba. Da misalin k’arfe 8:00AM Ummimi ta tashi se had’a akwati take sam nida Shettima bamu damu ba acewarmu ko tafiya zamui duka sede naga kayakinta kad’ai take ta had’awa dana tambayeta in zataje kuwa ba kunya ba tsoron Allah ba tausayi ta kalli cikin idanuna tace min *talaucin mahaifinku ya isheni tattara kayakina nake saurayi na zezo ya d’auke ni in tafi inbar nan* atake kaina naji ya soma juyawa wace erin magana Ummimi take dama mata masu aure sunayin saurayi ne? Danni ban tab’a jin malamin islamiyan mu ya fad’a mana ba. Sema na d’au wasa take na shareta mukaje muna ta wasa nida Shettima. Abuu na zaune a Parlour ya tambayeni. Anas Baba na ina mamarku? Ko yau d’inma ta fita ne? A’a Abuu tana d’aki tana shirya kayakinta tace min wai saurayinta ze zo ya d’auketa. Take Abuu ya mik’e what!? Niko na sake nanata masa. Bada dad’ewa ba sega Ummimi tafito tana jan akwatinta.]_ _[Aysha ina zakije haka? Aww d’an naka bai fad’a maka bane? Tafiya zan saurayi na na jira na. Haba! Aysha wace erin magana kike? Wani erin saurayi kuma? Cewar Abuu]_ _[Ai kasan sa Alhajin Yola, shi nake nufi, rayuwar talaucin nan ya isheni ni tafiya zan inje inji dad’in rayuwa na nima.” For the first time naga idan Abuu yacike da hawaye kafin in hankara naga yana kuka take nima na fara same goes to my brother. Rok’arta na soma haka Shettima ma banda Abuu dayayi mutuwan tsaye.]_ “Huhhh!!! Nagaji I'll continue some other day.” “Haba! mana maza da Allah k’arasa mana.” Cewar Musty. “Nace maku I'll continue tomorrow or later I promise, baki na yagaji da surutu kunfi kowa sanin ban cika magana ba ai nayi k’ok’ari ko?” “Sosai kayi Anas namu me blue shining eyes. Yi hak’uri ka gama mana amma” Abdoul ya fad’i yana masa zak’in bak’i. “Okay toh siyo min soda sena cigaba ishi nake ji.” Ba musu Abdoul ya tashi ya siyo masa ya dawo da sauri. “Gashi toh cigaba muna jinka please.” Bayan ya bud’e sodan ya kwankwad’e tas sannan ya cigaba kamar haka; *©miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [16:09, 12/19/2016] Swtbaby: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 1⃣0⃣ “Last words da mukayi exchanging da ita are forever stuck up in my head.” _[“Ummimi dan Allah karki tafi kiyi hak’uri indan plates dana fasa ne I promise baran sake ba. Ummimi I am sorry dan Allah karki tafi. Abuu ka hana Ummimi tafiya dan Allah kace mata I will be a good boy from now on.”]_ “Haka nata had’ata da Allah ko saurarena batayi ba” _[“Yanzu Aysha bara kiji tausayin yaranki ki hak’ura ki zauna dasu ba? Kalli yadda suke kuka fa?”]_ cewar Abuu _[“Mstww wannan kuma ku ya shafa nagaji da zama cikin talaucin nan, ace kullum se atashi ba’a san me za’a karya dashi ba gaskia nagaji daman tun farko sanda Abba na yace kar in aureka matsiyaci ne kai amman nak’i sauraronsa. Ga can miji Allah yamin har k’asar waje ze kaini saboda haka ban ga abinda zesa in cigaba da zama a wannan gidan ba.” Jakarta ta ja ta soma tafiya da sauri naje na kama k’afarta ina kuka ina rok’arta. “Ummimi please don’t leave us we love you dan Allah karki tafi, Abuu will find a better job dan Allah karki tafi...” wani wawan ball tayi dani da k’afa nafad’i na ji ciwo a elbow na har d’inki sanda aka min wajen...”]_ “Kun ga ci won?” Ya mik’o hannunsa ya nuna masu Musty. Ciwo ne babba sosai ace yau shekaru kusan goma amman hakan besa ciwon ya rage girma ba. Komawa yayi yasake kishingid’a. _[ko waiwayo wa ta dubani batayi ba jakarta taja ta fice, asibiti Abuu yayi rushing d’ina. Tun daga ranan Abuu ya rasa walwala, Abuu da mukasani da fara’a da murmushi ya koma wani abu daban. Kullum cikin tunani, nida Shettima tun tafiyar Ummimi muka rasa gatanmu, kakarmu bata raye bale ace ita zata kula damu, abinci ma waninsa’in mancewa ake damu haka zamu kwana da yunwa Ummie sister’n Abuu ce data dawo daga Maiduguri tayi alk’awarin zama damu. A lokacin ina primary 5 zamuyi common entrance, ikon Allah ne kawai yasa nayi passing exams d’in saboda tafiyan Ummimi yayi affecting d’ina psychologically, mentally and socially.]_ _[Tun daga lokacin na canza, na dena dariya, nadena wasa koda da Shettima ne kullum cikin tunani nake har wani psysho psycho na soma zama. Ganin haka Kaka yabawa Baba shawara akaini Maiduguri Boarding school a tunaninsa in ina cikin yara zan sake, unfortunately koda aka kaini can abun nawa be ragu ba sede worse da yayi ma, bana cin abinci bana magana da kowa karatu na kawai nakeyi saboda blue eyes d’ina yasa yara dayawa suna san zama friends dani ace warsu ma ni bature ne sam bana basu chance guda biyu ne sukaci galaba a kaina Baana da Kashim, su biyu kawai suka samu na sake dasu muka zama friends.]_ _[A lokacin da mukayi second term hutu bayan na dawo gida na tarar da Ummie da jaririya kuma a iya sani na Ummie bata da aure. Tambayarta nayi ko ‘yar wace me kama dani haka amsar data bani ne ya mugun sake tada min hankali.]_ _[“k’anwarka ce Anas, uwar ku d’aya uban ku d’aya. Shekranjiya Ummimi tasa wani almajiri ya turo ta cikin wata basket da wasik’a.” Zafaffun hawaye ne suka soma gangarowa kan kumatu na. “Mesa Ummimi zatayi haka Ummie? Mesa barata tausayawa wa baby’n nan ba? Me tamata itakuma da zata rabata da d’umin jikinta? Mesa Ummimi ta tsane mu haka Ummie?”]_ _[“Anas nima bansani ba hak’uri zakayi, I'm here for you guys, bar kuka Baba na.” “Ina wasik’ar Ummie?”_ _Na tambayeta._ _Acikin wata drawer ta d’auko ta mik’a min na karanta kamar haka...]_ _[Ibrahim ‘yar da ke cikin wannan basket, ‘yarka ce da cikinta nabar gidanka. Allah ya taimakeni nasamu na haifeta ga abinka nan na kawo maka, banasan abinda ze sake had’ani da kai ko da ‘ya‘yanka...]_ _[Hawaye ne suka soma sauk’owa kan kumatu na hannu na mik’a na amshi sister na da ko suna Abuu be sa mata ba dan tashin hankali. Hawayen idanuna na d’iga kan fuakarta ta bud’e idanunta a hankali tana kallo na se kamar Ummimi nake gani, *Amal* na kirata dashi ina hawaye. Daidai lokacin Abuu yashigo. “Amal kasa mata Anas?” Alokacin ban fahimce abinda yake nufi ba sanda na tambayesa yake fad’a mun yak’i sa mata suna ne saboda ni yake jira nayi naming nata tunda nace mata Amal sunan ta Amal kenan. Tun daga ranan na d’au alk’awari zanyi protecting Amal da raina, zan zame mata uwa.]_ _[Ban tab’a jin inason d’an Adam kamar Amal ba, simply because of tausayin da take bani har yau bata san tanada wata mahaifiya bayan Ummie ba, rok’ar Abuu nayi kar a fad’a mata gaskia banasan rayuwarta ta tab’arb’are kamar yadda nawa yayi. Komai ni nake wa Amal har noma nafarayi tun ina d’an yaro in nayi harvesting se in siya wa Amal kaya da kauan abinci as Abuu har a lokacin be samu aiki ba. Tun tana k’arama take sona ko kuka takeyi ina amsarta zatayi shiru kwana ma tare mukeyi da ita, ko yawo zanje da ita nake zuwa. Sam banso komawa makaranta ba da hutun mu yak’are gudun kar nayi missing nata. Ba yadda na iya haka na koma amman kullum da tunaninta nake kwana in tashi.]_ _[Ina jss 3 aka sa Shettima a school namu, jiki na jasa sosai ko kad’an bana barin school bullies su tab’a sa. Abokai na abokansa ne. Alokacin Abuu ya samu aiki rayuwar mu yasoma canzawa a hankali ya gina mana gida Amal kuwa se girma takeyi a lokacin tana da shekaru biyu da abu akai. Amal completes me, kullum tare muke da ita duk sanda nazo komawa school setayi kuka tace seta bini. Har dan haka nad’au alk’awarin barin sake dawowa gida ba se nagama school d’in gabad’aya bana san ganin kukan Amal. 3 years later nagama secondary school I was 16 years then Shettima kuwa yana ss1 time d’in. I can’t believe Amal dana ganta she was 5 years then, ta girma sosai in na ganta kaina kawai nake tunawa da muguwar Ummimi.]_ “Tun daga lokacin na cigaba da kula da sister na har ila yau. Ummimi kuwa bamu sake jin labarinta ba tunda ta bar gidanmu yau about 10 years kenan.” Numfashi ya saki tare da tasowa daga kan kujerar ya mik’e tare dayin mik’a “kunji labarina you guys are the first to know. Kunji dalilin dayasa na rasa happiness d’ina, dalilin dayasa na tsani Ummimi da kowace mace banda mata guda ukun nan; Amal, Ummie seda yarinyar danayi blaming nata akan laifin Ummimi har nayi raping nata wanda har yau ban san ya take ba, bansan kona kasheta ba bansan irin ciwon dana ji mata ba. I can’t ever forgive myself for what I did to her har se ranan dana ganta na nemi gafararta ta yafemin. She was just 15” “Anas stop blaming yourself, ba’a cikin hankalinka kayi mata abinda ka mata ba in shaa Allah bata mutu ba someday in the future zaku had’u kuma zata yafe maka inhar ka bata labarin ka. Gaskia Anas kasha gwagwarmaya a rayuwarka, kayi witnessing bak’in cikin rayuwa at a very tender age. Ummininku sam bata kyauta muku ba.” Cewar Abdoul cike da tausayawa wa Anas ashe saisa kullum yake cikin tunani baya dariya, he has been through so much ba laifinsa bane because of how he is now. “Anas if only zan iya taimaka maka da nayi, you've had such a horrible past just know that when ever you need a shoulder to cry on we are here for you.” Musty yayi assuring nasa. Kallonsu Anas yayi tare da ciri sunglasses nasa rana ya haska blue eyes nasa da skin nasa yayi kyau sosai. Murmushi ya saki kad’an wanda ya bayyano da fararen hak’waransa “thank you guys, so now what? Kun ga laifi na saboda nace na tsani mata barin yi aure ba?” Kai duk suka kad’a “wallahi ko k’adan Anas you have every single right ka tsani mata fiye da komai sede inda zaka yayyafa wa zuciyarka ruwan sanyi you can find love in your own way I'm sure Allah ze sak’a maku abinda Ummimi ta muku by kawo maku matan da zasu kula daku su soku tsakani da Allah badan kyanku ko kud’inku ba but tsakani da Allah and barasu tab’a barinku ba kai da wanka Shettima se mutuwa.” Cewar Musty. “Sosai dude Musty is absolutely right.” Abdoul ya mara wa Musty baya. “Ofcourse you guys are right, but niko kad’an I don’t have faith in love to talk more of marriage, I wish to finish my life single ba senayi aure ba. Dama ai ana aure ne dan a haifafa I have Amal, she is like a daughter to me.” Musty ze sake magana Anas ya katsesa by changing topic of discussion d’in. “Yau da kuka sani na tono past d’ina dole se na sha 2 bottle na syrup d’incan if not barin iya bacci ba and also I feel like drinking yau muje bar (gidan giya) mud’an tab’a flavours da suke dashi.” Tsaye sukayi duka suna masa murmushi sannan suka fice... *FANNAH* _One week later..._ Bam! bam! bam! bam! bam! “Salamu alaikum!! Salamu alaikum shin ba kowa ne a gidan?” Cewar Ya Khaleel dayafi kusan minti uku tsaye a bakin k’ofar gidansu Fannah yana sallama da knocking. Mami dasu Afrah sun fita, Fannah da Baba kad’ai a gida, Baba kuwa jikin sa yayi worse yau ko magana bai iyayi yana jin knocking da sallaman amman ba halin amsawa musamman ma dayaji Ya Khaleel ne. Fannah kuwa tana bayi tana wanka se sauri take tafito ta amsa sallamar. Bayan minti biyu tafito daga bangidan har yanzun sallaman Ya Khaleel yake, hijabi ta d’aura kan towel dake jikinta gashin kanta dana jikinta duk sun jik’e kwance a jikinta. Da sauri ta fito “wa’alaikumussalam sannu da zuwa Kawu.” “Se yanzu kika ga daman fitowa?” “Kawu wanka nake-” Katseta yayi “rufa min baki! Allah sa de ba na miji kika b’oye cikin d’akin ba.” Da mamaki ta d’ago kai ta kallesa shima kallon nata yake wani kyantan ma se yau ya soma gani, gashin girarta da suka had’e sun kwanta kan fatar ta me uban haske. Haka sajen fuskarta ma. He can’t wait Fannah ta haifo masa jikoki kyawawa kamar ta. “Ina sauran ‘yan gidan kuma suke?” “Sun fita unguwa” tabasa ansa a takaice. “Aww kekuma fah? Ai! Na tuna ashe baki fita yanzu saboda kar aganki a kiraki da sunanki karya ko? Anyways ina Baban naki yake? Inade be mutu ba tukun? Kice masa ya d’an k’ara k’ok’ari yajira yaga bikinki da Farouq. Nazo ne in sanar daku bikin ki da d’an nawa nan da wata d’aya ne nagama duk abinda nasan ya kamata komai na sai muku gado nede banyi ba. Wannan kuma keda iyayenki zakuyi bandamu ba koda sata zakuyi kokuma sayar da ‘yarku me uban bakin nan. Ni na tafi” Fannah bata ce komai ba illa hawayen dake forming a idanunta. Har ya juya ya soma tafiya sekuma ya dawo yana kallonta. “Bakice komai ba ko baki jini bane? Kokuwa rashin kunya kike ji dashi?” Ya jefa mata wannan tambayoyi. Hannu tasa ta share hawayenta, “A’a Kawu ko k’adan, kayi hak’uri kuma mungode in Mami ta dawo zan sanar da ita.” “Yafi kam ki sanar da ita tun da wuri inma sata zatayi tayi ta had’a miki kud’in gado kokuwa kina kwana a k’asa in anyi auren dan Farouq da gadonsa ze tafi.” Yan kaiwa nan ya fice. D’aki ta ruga a guje ta baje kan katifarsu ta soma kuka, kuka take sosai abin tausayi. “Bawan Allah mesa ka amshe min martaba ta? Mesa ka rabani da budurcina? Mena maka? Mesa se ni? Mesa ka juya min rayuwa ta upside down haka? Mesa se ni? Dalilin abinda kamin kasa rayuwata ta koma wani abu daban, banida gata banida ‘yanci banida masoya banida komai...” Ta kuma fashewa dawata erin matsanancin kuka. Ita da mutuwa zatayi dayafi mata akan auren Ya Farouq tasan definately kasheta zeyi a gidansa in har ta auresa ko a yanzun ma bai ragar mata ba bale ace tazama mallakinsa. *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [16:09, 12/19/2016] Swtbaby: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 1⃣5⃣ ★★★★★ _5 months later..._ Shak’uwa ne me k’arfin gaske ya shiga tsakanin Anas da Mr. Muh’d, ladabi da biyayya kam Anas ya iya duk wanda yaji ana cewa Anas na shaye-shaye ze k’aryata zancen. Basu tab’a samin matsala da Mr. Muh’d ba aikinsa duk yanayi me kyau tun da yayi joining enterprise d’in abubuwa suka sake improving fiye da da. Family’n Anas a yanzu haka sun dawo Maiduguri da zama a unguwar New GRA. katafaran gida Abuu ya sai masu da taimakon Anas. Gida ne mansion d’aki kota ina. Rayuwa alhamdulillah yanzu, ansa Amal a Ruby Springfield College. Shettima kuwa ya soma attending UNIMAID a inda yake karanta accounting. Anas yayi introducing family’nsa wa Mr. Muh’d sosai suka shak’u da juna. Sanin yadda Anas keson Amal yasa shima Mr. Muh’d yakeson Amal sosai, musamman yadda take sasa dariya duk sanda suke tare in su Anal sunyi hutu kullum tana office wajen Mr. Muh’d datake kira da grampa, wane family haka suka zama. A birthday’n Anas Mr. Muh’d ya basa sabuwar mota pil cikin leather k’irar mercedes-benz SLK. Tunda Anas yayi mota walak’anci ya k’aru ahaka yanzu a list nasa yanada mata 33 da yayi breaking hearts nasu. Leaving life nasa yake to the fullest duk sanda su Baana suka shigo Maiduguri kuwa shan giyan ranan na daban ne. Suna waya sosai da friends nasa Abdoul da Musty. Yau ranar ta kasance Monday as usual ya soma shirin office, Shettima da ba lectures se da rana se bacci ake sha. Amal da ba office zata ba amman ta riga Anas tashi tare suka had’a breakfast su biyunsu sukaci bayan sun gama ta rakasa har parking lot yashiga cikin sabuwar motarsa sukayi ba-bye da juna sannan ya fice. As usual yashirya wa Mr. Muh’d schedule nasa na ranan yakai masa. “Welldone Anas, kana k’ok’ari sosai nace zanen project d’incan kasamu kayi kuwa? Kasan mutanen daga Ghana zasu zo yau akoi board meeting da za’ayi by 4:00PM zamu masu presenting.” “Eh Baba nayi yana nan ajiye cikin shelf a store room floor 2.” “Good, se meeting d’in zanbar care d’in a hannunka. Akoi inda ake samun professional waiters a Fahmaz coffee shop (inda Fannah ke aiki) kayi waya da masu wajen kamana booking. “Okay Baba, I’ll be going” nan ya zarce office nasa inda ya kira number’n me Fahmaz coffee shop d’in. ***** “Ya Suleiman ga call from Flames Enterprises.” Fannah ta danna kira wa Ya Suleiman dake waje. “Ki d’aga kiji meneh, I'm busy here.” Hannu tasa ta d’aga tare da yin shiru bata ce komai ba. “Hello?” Anas ya fad'i cikin muryarsa me tafiya wa kowace mace da imani. “Hello” Fannah ta fad’i in return. This is Fahmaz Coffee shop, how can I assist you?” Jin muryar mace ne yasa ransa ya b’aci take. A fusace yace, “ai nasan Fahmaz Coffee shop d’inne saisa na kira so just shut up plus haka aka koya miki wajen aikin naku in kun d’au waya kuyi shiru?” “Lalle ma wannan mutum anyi d’an iska” cewar Fannah a zuci “shi ya kira kuma yana jiran nice in soma yin magana?” Dukda bame san magana bace amman taji barata iya hak’ura ba so take ta sa koma waye ne shi in his rightful position sekuma ta tuna wannan business related matter ne she shouldn’t take it personal. “I'm sorry. How can I assist you?” “Mstchww” yaja tsuka sannan ya cigaba “we need 5 waitresses and 5 waiters from your coffee shop here at Flames Enterprises by 4:00PM.” “Okay copied” tace. “Bama tolerating late coming you guys should make sure 4 d’in ya muku anan.” “Lalle ma wannan mutumin” cewar Fannah a zuci. “Ko baki ji bane?” Zatayi magana ya katse dagangan. Ciro telephone d’in tayi daga kunnenta tana kallon wayar cike da namaki wannan wani irin bawan Allah ne me uban jijji dakai haka? Mstcw taja tsaki daidai lokacin Asma’u ta shigo “yau Fannah ke tsaki? Keda waye ne haka?” Ta bud’e baki zatayi magana Flames Enterprises d’in yasake kira sanda ya kusan tsinkewa sannan ta d’aga “yes.” “Don’t use that tongue with me young lady” cewar Anas in a serious tone daya tsorata Fannah kum tayi shiru. “Incase clueless mind naki be baki idea ba, you have to be here now saboda coffee zakuyi serving ba drinks ba. So zakizo in baki details d’in plus don’t be late bana jiran mutum sede a jirani.” Shiru tayi tana mamakin wannan bawan Allah. “Are you there? Cause bana repaeating kaina twice” “Yes I’ll be on my way.” Nan ya katse wayar. Tsuka takuma ja “lallai akoi arrogant people dayawa a duniya what is he feeling like? D’an Adam de ba wanda yafi wani we are all equal.” Asma’u dake kallonta tace, “ji yadda kike magana sekace bakisan Anas ba.” Fannah tace, “Anas? Waye shi?” Asma’u tace, “no wonder sesa kike tada jijiyoyin wuyanki haka, ni rananda ya kira na d’aga bakiga zagin duniyan daya min ba aike yamiki mutunci ma.” “Toh waye shi? Whats he feeling like?” “Shine PA’n Mr. Muh’d na Flames Enterprises kuma ance Mr. Muh’d nasan sa tamkar d’an cikin daya haifa, cewa ma yake Anas d’in d’ansa ne.” “Ikon Allah! Lallai kam.” cewar Fannah cike da mamaki. “You better go kafin yasake kira ya balbale ki.” A sanyaye Fannah ta fice bata tsaya ko inaba se Flames Enterprises can akayi directing nata zuwa office na Anas tsaye take a bakin k’ofar office nasan takasa shiga zuciyarta se bugawa take musamman ma data d’aga kai taga ansa *Mr. Fauzy* asaman. Tafi minti biyu tsaye a wajen sannan jiki na k’yarma hannu na b’ari tayi knocking k’walli d’aya tal jin ba’a amsa ba yasa ta k’ara d’aya “come in” taji muryan na miji ya fad’i authoritatively. Tabbas tasan wannan murya shine wanda yace mata thank you rananda Mr. Muh’d ya bata bandir na N500 kawai haka taji zuciyarta na bugawa tarasa dalili. Numafashi taja sosai sannan ta bud’e tashiga. Wannan office shi ake kira da Aljannan duniya tana shiga k’amshin turare ya buga mata hanci ga wani uban sanyin da office d’in ya d’auka ko ina tsatsaf yake files, papers da books duk anyi arranging nasu. Hijabinta iya guiwa takuma daidaita sa sannan tayi sallama. “Salamu alaikum” mutum ta hango kan kujera da P cap (facing cap) akansa wanda ya b’oye kamanninsa. Sanye yake da black long sleeve shirt wanda ya mugun amshe farar fatarsa me kyawun gaske. Yanada fad’i dadai, na matashi ne me jini a jik’a. Laptop ne a gabansa se faman danne danne yake akai he is si focused akai, can yad’an tsaya ya sha wani abu cikin cup wanda Fannah batasan ko ruwa ne ko juice ba can ne tagane ashe soda ne. “Zaki iya dena kallo na haka dan ba TV bane ni, and you don’t knock and say Salamu alaikum all at thesame time you choose either one.” Ya fad’i batare da ya d’aga ido yaga kowaye bane. Kunya taji kamar ta nitse k’asa dan kunya “taya yasan ina kallonsa toh?” Ta tanbayi kanta a zuci. “I'm sorry” ta fad’i cikin muryar ta dake b’ari. *I'm sorry nasan chapter’n nan yayi gajere sosai compared to other chapters d’in bayan nawa ne har yanzu na ciwo. In shaa Allah zan yi k’ok’ari inyi dayawa gobe. Thank you for the lovely prayers and warm concern. I love you all* *© miemiebee* beeenovels.mywaoblog.com [16:09, 12/19/2016] Swtbaby: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 1⃣1⃣ Bayan tafiyan Ya Khaleel bada jimawa ba su Mami suka dawo gida, Fannah na d’aki tana kukan cire rai bata ma ji shigowansu ba kawai ganin Mami tayi tsaye a kanta take ta soma share hawayenta “sannu da zuwa Mami, yaushe kuka dawo?” “Habibti kukan me kuma kike? D’an mayen can yazo ne?” “A’a ba kuka nake ba Mami, inasu Afrah?” “Fannah ga idanunki sunyi ja sun kunbura, fad’a min meneh? Keda waye?” “Ya Khaleel ne yazo...” Nan ta irga mata duk abinda yafaru tana kuka. Rungumota Mami tayi “Shikenan yi shiru in shaa Allahu Kawu da d’ansa barasu k’arisa da duniya lafiya ba, mugayen mutane kawai bar kuka kinji? Akoi Allah Fannah always have this at the back of your mind, in shaa Allah baraki auri Farouq ba.” Hannu tasa ta share hawayenta, “Mami ni nasan zan auri Farouq ba abinda zamu iya Ya Khaleel yariga ya gama komi.” “Fannah kin cire rai daga Allah kenan?” Kad’a kai Fannah tayi “toh ki bar fad’in haka, Allah ba azzalimin bawansa bane. Allah da kansa yace a Qur’ani auren mazinaci se mazinaci aikinsani koh?” Kai Fannah ta giad’a “toh kibar kukan ya iso mik’o mai in taje miki gashinki.” A sanyaye ta mik’e ta d’auko mai da comb mama ta taje mata gashinta takama mata gu d’aya sannan ta bata waje tasa kaya. Itakuwa ta fice zuwa d’akin Baba. Kwance ta samesa, “Malam ya jikin?” Baki na k’yarma yace, “da sauk’i.” “Sannu, Malam ko kanada labari d’azu Kawu yazo ya cicci mutuncin Fannah? Duk nazo na sameta se kuka take.” “Eh..Mam.. Maman Aiman saisa yazama dole in siyar da gwalagwalen da Umma (mahaifiyarsa) ta tab’a bani dana ajiye kan duk sanda Fannah tazo aure se in sayar mu mata kayan d’aki amman tunda ga yadda abu ya kasance dole mu siyar yanzu...” Tari ya tsaya yayi sannan ya cigaba. “K’ark’ashin wancan akwatin akoi d’an kunne da sarqa da zobe dakuma warwaro guda hud’u na gwal, da ace ina da lafiya da a gobe zan jeni Maiduguri in siyar amman gajan haka yasa dole seke zaki Maman Aiman.” “Ina jinka Malam, in mun siyar me zamu da kud’in?” “Gidan nan zamu bari, garin nan zamu bari gaba d’aya mukoma Maiduguri inason bayan kinje kin siyar da gwala gwalen ki kama mana gida me arha koda 2 bedroom ne kawai wanda zamu iya affording, sekuma da essential abubuwan da zamu iya bu-” tari ne ya tsaida sa sosai. “Malam shikenan ya isa nagane kar jikin ka ya tsananta. Amman Malam bara mu tafi da kayakin mu ba? Inaga zefi mana sauk’i inda hali ma gidan nan se mu siyar.” Gyaran murya yayi sosai “inaaa... hakan bame yuwu wa bane Maman Aiman mukayi haka ai kamar mun fad’awa duniya zamu bar garin Bama ne kisani no one must know about this. Fannah kawai na yarda ki fad’a mata itanma dan mu cireta daga damuwa ne kuma ki gargad’e ta karta kuskura ta fad’awa Afrah kar da baki taje cikin jama’a ta tona mana asiri. Dan maganan nan na fitowa fili shikenan namu ya k’are dole Fannah zata auri Farouq, ni na fad’a miki.” “In shaa Allah Malam, Allah kaimu goben zan wuce Maiduguri dan kasan matsalar samun gida, in bamu soma nema a kan lokaci ba zamu makara har lokaci ya k’ure we have just a month.” **** “Fannah habibti. Fannah!” Kirar Mami dake tsaye daga bakin k’ofa. Sanda Fannah takai k’arshen ayan datake karantawa sannan ta amsa “na’am Mami am sorry bansan yanke ayan ne.” “Bakomai karatu kike ne?” “Eh Mami wani abu ne?” “Ina Afrah da Aiman?” “Suna can parlour suna assignment.” Fannah ta amsa a takaice. “Oh toh magana daman nazo miki.” “Toh bismillah Mami” nan Mami ta k’ariso ciki tare da rufo k’ofar tayi joining Fannah kan katifar sanan a hankali ta sanarda Fannah abinda ita da Baba ke da shirin yi. Sosai Fannah taji dad’i harda hawayen nin dad’i. “Mami dagaske kike? Zamu koma Maiduguri barin auri Ya Farouq ba?” “Sosai Habibti ai dama na fad’a miki koda bamuda komai munada Allah, kuma Allah ba azzalimin bawa bane kamar yadda na fad’a miki gobe zani Maiduguri.” “Toh Mami in bi ki mana muje tare.” Cewar Fannah tana share hawayen jin dad’i. “A’a Fannah kinsan Kawunki wane bodyguard haka yake kusan kullum seya zo gidan nan inkuma yazo bani ba ke kinsan dole yayi bincike the moment asirin mu ya tonu kuwa kinga dole sekin auri Farouq. Saboda haka ni kad’ai zanje addu’a kawai zakimin Allah sa inje a sa’a in dawo lafiya.” “In shaa Allah Mami Allah baki sa’a. Nagode sosai, keda Baba kun gama min komai aduniya Allah biyaku da gidan aljannah.” “Ameen Habibti barin koma in had’a akwati na.” “Toh muje in tayaki shiryawa.” “A’a Habibti zanyi dakaina, go on da karatunki.” “Toh Mami.” Har Mami takai bakin k’ofa Fannah ta danna mata kira da “Mami!” “Na’am Fannah.” Ajiye Qur’anin dake hannunta tayi ta ruga gun Mami da gudu tayi hugging nata “Jazakumullahu bikhairan keda Baba nagode sosai, Allah sak’a muku da gidan Al-Jannah.” “Ameen Habibti Allah miki albarka kema.” “Ameen” ta ce sannan ta sako Mami tana kallonta har sanda ta shige d’akinsu da Baba. Sujjada tayi tana gode wa Allah sannan tashiga bayi tayi alwala tayi nafila raka’a biyu tare da sake gode wa Allah ji tayi kap matsalolinta sun gushe. Kan katifar su ta fad’a se murmushi take. **** _4 days later..._ “Oyoyo Mami! Oyoyo Mami!” cewar Aiman tana daka tsale. “Oyoyo auta ta” Mami ta d’aga ta sama. Nan su Fannah suma sukazo suka mata oyoyo. Kwanan Mami uku a Maiduguri tadawo, tafiyar ta kuwa was a success kap addu’o’insu Allah ya amsa musu. Kud’in data samu bayan ta sayar da gwala gwalen ta kama musu gidan haya 2 bedroom dashi a unguwar jiddari polo, na shekara, seda katifu guda biyu da d’an kayan abinci da kayan kitchen. Alhamdulillah! _2 weeks later..._ Farouq ne tsaye bakin gidansu Fannah shi a dole yazo ganin matarsa nan da sati d’aya da ‘yan kwanaki zata zama mallakinsa tsabagen iskanci ba abinda yake imagining illa first night nasa da Fannah. Wani almajiri ne yazo wucewa take ya tsaida sa “kai shiga nan kace wai inji Farouq matarsa ta fito.” Da “toh” yaron yashiga gidansu Fannah suna zaune tsakar gida suna tsintar shinkafa ita da Afrah. Ita kanta Afrah mamakin yadda Ya Fannah ke walwala kwana biyu ke bata kukan data sobayi safe rana dare yamma duk tadena yanzu, dukda batasan reason nayin hakan ba itade tana ma yarta murnan dawowar farin cikinta. “Assalamu Alaikum” cewar almajirin. “Wai inji Farouq wai matarsa tafito” dadai lokacin Mami tafito daga kitchen. “Me kace?” “Farouq ne ya aiko ni wae matarsa ta fito.” “Dan ubansa kace barata fito ba yaushe tazama matartsa? Fice kabani waje.” “Almajiri tsaya” cewar Fannah “kace masa ina fitowa.” Kallo Mami ta watsa mata “Fannah baraki fita ba kinsan wannan d’an mayen yanzu seya saki kuka ki zauna.” “A’a Mami kibari inje ai ba abinda ya isa yamin a waje a idan mutane, kiyi hak’uri.” Mami zata sake magana Fannah tace, “please Mami.” Da d’aga kan da Mami tamata Fannah ta shiga ciki ta d’au hijabinta sannan ta fice a zaune ta samesa kan benchi da alama yau ba a buge yake ba. “Ke zo nan kizauna yaci ace kin saba dani yanzu, nan da ‘yan kwanaki zaki zama tawa.” A zuci Fannah tace, _taka? never! Allah ya riga ya kare ni daga auren mazinaci kamar ka._ Kawai jin hannun sa tayi kan kumatunta firgit ta matsa baya. Yasake matsowa kusa da ita “wai tunanin me kike haka? Kode tunanin first night namu?” Ya d’an murmusa “karki damu I'll take it easy on you” batace dashi komai ba illa kallonsa da take. “Ke wai yau azumin magana kike ne?” Juyawa tayi zata tafi ya danna mata kira cak ta tsaya bata tanka sa ba. “Kiyi sha’aninki iya san ranki kimin rashin mutunci iya san ranki amman kisani nan da sati d’aya da ‘yan kwanaki ni zanna ja miki aji. You can go daman nazo inga kyakkywar fuskarki ne kafin na wuce bayan gari.” Kai kawai takad’a tashige ciki. Tsaye ta tarar da Afrah da Mami da damuwa karara a fuskarsu. “Ya haka Mami wani abu ne?” Ta tambayesu “Farouq fa inade be miki komai ba?” Cewar Mami. “Kai Mami da Allah ki kwantar da hankalinki Mami, kema haka Afrah ba abinda Ya Farouq yamin banda suratan banzan daya saba wai yanzu haka ma bayan gari zasa.” “Shege mazinaci” cewar Mami. “In shaa Allahu baraki auresa ba.” “Amman Mami yau fa sauran sati d’aya da kwana uku ne bikin anya akoi abinda ze hana aukuwan wannan aure?” Afrah ta fad’i cike da damuwa. “Akoi Allah Afrah, always have this at the back of your mind. Jeki huta Fannah nida Afrah zamu gama girkin.” “Toh Mami, ina Aiman tazo mu mata tsifa.” _3 days later..._ Ana saura sati bikin Fannah da Farouq. Ya Khaleel ne tsaye cikin tsakar gidansu Fannah. Mami, Fannah da Afrah suna tsaye kansa. “Toh nide nafad’i nawa tun ana wata bikin nan na fad'awa Fannah ta sanar dake batun gadon nan gashi har yau baku sai ba wallahi zakusha mamaki dan kuwa amaryarku kan tabarma zata kwana. Wasu erin matsiyata ne ku? Ace ‘yarku zatayi aure ko gado kun kasa yi mata? Wai ahaka ma dan na d’auke maku nauyin kayan kitchen. Allah wadar in erinku wallahi.” “Kawu kayi hak’uri nan da ‘yan kwanaki zan kwashe adashe na se in sai wa Fannah gadon dan Allah ka k’ara hak’uri.” Cewar Mami. “Wannan kuma ku ya dama, ko ku sai gado ko amaryarku tayi kwanan tabarma. Ni na tafi.” Yana ficewa Mami taja hannun Fannah sukayi d’aki gudun kar Afrah ta fahimce wani abun. Itade Afrah tasoma zargin abu da a da ne Kawu yayi wannan magana definately Fannah zatayi kuka sega yau ko nuna damuwa batai ba. Da daren ranan Fannah da Afrah suna zaune d’akinsu Aiman tayi nisa a bacci. Afrah tafi minti biyu tana kallon Fannah har sanda tasa ta tsarguwa. “Afrah wannan kalo haka?” Cewar Fannah tana duba pages nawani Government text book. “Ya Fannah kallen.” D’ago fararen idanunta tayi wanda suka sha bak’in kwalli ta azasu kan Afrah. “Na kallekin” tace. “Kina b’oye min wani abu kinsan na sanki fiye da yadda nasan kaina I can tell in kina b’oye min bu.” Cewar Afrah “Me zan b’oye miki Afrah? Kawai de inajin dad’i ne.” “Dad’in me fah? Dad’in zaki aura Ya Farouq??” Ta tambaya tare da d’age gira. Dariya kad’an Fannah ta saki “ko kad’an Afrah ina murna ne saboda inaji ajikina barin auri Ya Farouq ba.” “Toh Ya Fannah Allah sa, kinsan happiness naki ya fiye min komai a duniya.” Hugging junansu sukayi cike da so da k’aunar juna. **** _Ana saura kwana biyu biki..._ Da misalin k’arfe 8:00AM “Farouq! Farouq!” Kiran Ya Khaleel yana zaune kan tabarma. “Na’am Baba” Farouq ya amsa yana isowa sannan yasamu waje ya zauna. “Ni ya jiya ka had’u da Fannah kuwa? Mahaifiyarta tace mun cikin satin nan zasu kawo gadon gashi saura kwana biyu bikin naku basu aiko ba. Anya mutanen nan lafiya kuwa?” “Ni Baba kawai mu share zancen gadon nan kafa san basuda kud’i ni Fannah ta zamo mata ta shine babba ban damu ba ko kan tabarma zamuna kwana bale ma ai ina gado se in tafi mana dashi.” K’eyarsa Ya Khaleel ya tand’e “ai dama kai wawa ne, taya mu zamu masu komai tashi muje gidan nasu yanzu.” Ba gardama Farouq yabi bayan Babansa suka fice zuwa gidansu Fannah. “Salamu alaikum!” Cewar Ya Khaleel a yayinda Farouq kuma ke knocking shiru kukeji ba amsa “waiko wannan matsiyatan bacci suke ne?” Ya Khaleel ya tambayi Frouq. “Toh ya zansani Baba inba wai shiga zamuyi ba.” Sa kai sukayi a tare Ya Khaleel na sallama sede har da suka iso tsakar gidan ba amsa dan haka Ya Khaleel yayi d’akin Baba yayi knocking nanma shiru hannu kawai yasa ya bud’e k’ofar yaga d’akin wayam! Daga katifa se katifa ba bakunan kaya ba komai. “Tashin hankali!” ya kira a fili. Farouq dake tsaye tsakar gidan yace, “lafiya Baba?” “Ba lafiya ba” cewar Ya Khaleel “zo kaga ba kaya a d’akin nan. Tsaya duba d’ayan d’akin yaran tukunnah” nan Farouq yaje ya bud’e same story. “Nan ma ba kaya Baba.” “Tashin hankali! Bade Aliyu da iyalansa sun gudu sun bar garin Bama ba.” Y fad’i cike da tashin hanakli. “Amman ai basuda inda zasu ma, through out rayuwarmu anan mukayi, baida ma kud’in biya masu kud’in mota bale ace ya kama masu gida a inda sukaje. Dole suna cikin garin nan suna b’oye cikin wani gida taho muje mu sami kakanka mu irga masa.” Bayan sunje sun samu kaka Ya Khaleel ya irga masa komai. Matuk’a Baba yasha mamaki. “Tunda haka d’an uwanka yayi deciding, mu barsa mu ga iya gudun ruwansa. Mun nuna masa halacci ya nuna mana butulci. Ni badan komai na amince da wannan maganar ba dan kar ‘yarsa ta rasa mijin aure ne amman tunda haka yace se mu barsa.” “Haba! Baba haka zakace!? Nida na d’au tsine masa zakayi. Guduwa fa yayi Baba ya bijire wa umarnin ka.” “A’a Khaleel ba maganan tsinuwa anan fatan mu Allah sa hakan dayayi shine mafi alkhairi garesa da ‘yarsa dakuma iyalansa gaba d’aya.” Ko “amin” d’inma Ya Khaleel be amsa ba shida yagama sa rai Fannah zata haifo masa kyawawan yara ace sun gudu basu gidansu. IMPOSSIBPLE. “Tashi Farouq yau ko shadda suka shiga suka b’uya semun tonosu bayan nagama bazawa a gari zakayi aure se ace amarya ta gudu wallahi k’arya ne tashi nace. Aliyu be isa ba yau duk inda suke a b’oye sena nemo su!” Baba na k’olla masa kira ko a jikinsa yaja hannun Farouq a fusace suka bar gidan. *Masu karatu kui hak’uri yau bansamu nayi typing kamar yadda na saba ba, severe back pain ke damuna in shaa Allah gobe zanyi dayawa. I love you guys!* *©miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:46, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 1⃣2⃣ Da misalin k’arfe 7:30AM su Fannah suka isa garin Maiduguri daga can suka tsara taxi se sabon gidansu. Ba laifi gidan gaskia yayi arha d’akuna biyu ne da bayi biyu dakuma kitchen. Fannah takasa b’oye murnanta, finally barata auri Ya Farouq ba. Ya Kaheel da d’ansa Farouq kuwa haka kaman zararru suka riga bin gida one-by-one a Bama su a dole suna neman Fannah da family’nta sam hankalinsa be basa Maiduguri su Fannah suka tafi ba. Har dare suna neman su Fannah ganin ba mahalicci se Allah yasa suka hak’ura suka dawo gida disappointedly. Fannah kuwa yanzu rayuwa yasoma mata dad’i, a hankali ita da family’nta suke settling a Maiduguri hankalinsu akwance basuda wata tsoro yanzu, Government school me kyau Mami tasamu aka zuba Afrah da Aiman. Fannah kuwa ko kad’an bata sa rai kan zata cigaba da makaranta ba se sanda Baba yayi suprising nata kud’in daya kamata abiya akaisa asibiti ya yafe kan Fannah tayi proceeding karatun ta. Admisson aka nemo mata a Polythecnic course na Business Administration. Sosai taji dad’i. Koda ta soma zuwa makaranta kuwa kullum cikin hijabi da nik’af take, mazan makarantar su basu ma san ya fuskarta take ba bale ace su gano kyawunta su soma binta. Haka Allah ya cigaba da yima rayuwar Fannah albarka, karatu take sosai ba wasa, Mami tana d’an sayarda irin gwanjon kaya hakan nan dashi suke cafanin gida. Baba kam jiki se worse yake ba kud’in kaisa asibiti a kullum burin Fannah ta gama karatu tasamu aiki ta kai Babanta asibiti. Ya Khaleel kuwa koda ya kira Mami a waya bata d’aukawa haka yagaji ya bari. Rayuwa de alhamdulillah... ★★★★ _4 YEARS LATER..._ ★★★★ Abubuwa da dama sun gudana a both rayuwar Fannah da na Anas. Fannah tanada k’imanin shekaru ishirin a duniya yanzu. Kyanta yagama fitowa, hips nata da dukiyar fulaninta daidai jikinta beyi yawaba kuma be kasa ba masha Allah. Fannah takai mace duk inda ake neman mace, shekarunta kusan biyu da gama poly tayi graduating under Business admin da excllent result. Sede aiki ne har yau babu ta kasa samu, duk wad’anda ake bata ba related to course nata bane daga baya dole ta hak’ura ta karb’a aiki as a waitress (me serving abinci ko drinks a shago kokuwa wajen taron jama’a) a wani babban coffee shop. Dad’in abin Coffee shop d’in nasu sananne ne sosai cikin garin Maiduguri yawancin meetings kokuma party ko biki da akeyi a Maiduguri a Coffee shop nasu Fannah ake zuwa a d’ibi waitresses kuma duk lokacin da akayi haka kud’i suke samu sosai. Da wannan take samu ta biya kud’in school fees na Aiman dana Afrah, amman de yanzu Afrah itama tagama makarantar tana neman kusan shekara da gamawa. Fannah na k’ok’ari sosai dan tasa Afrah a makaranta sede abun ya gagara, jarin Mami ya jima da karyewa lokacin da jikin Baba yatab’a yin tsanani dole ta tattara ribanta da uwarkud’in business natan duka aka kaisa asibiti. A takaice de yanzu Fannah ce breadwinner’n family’nta duk akanta sukayi depending. Allah sarki Fannah ‘yar Albarka Allah cigaba da miki albarka, ameen. Samari kuwa ba ta kansu take ba, sau afi a k’irga in aka d’ibesu serving food and drinks a meetings alhazai masu ji da naira suka ganta sesun neme ta amman saboda duk sanda ta tuna da past nata, ta tuna bata da budurcinta martabarta setaji barata iya k’ara yin soyayya ba saboda definately randa aka gano gaskia ita ba budurwa bace za’a guje ta abinda bataso kenan. Bature yace prevention ia better than cure sesa tun farko ma bata sa kanta cikin soyayyar. Daga wanda zata musu k’arya tace takusa aure se wanda zata ce musu tanada aure. Zancen mafarki kuwa har yau bata dena ba kusan kullum setayi mafarkin mutumin dayayi raping nata wai ya dawo ze sake raping nata, Mami kullum ke calming nata in tayi mafarkin rananda Mami batta kusa kuwa haka zata riga kuka tana b’ari har wayewan garin Allah, Allah sarki! K’arfe 2:00PM... Dadai lokacin tashin Fannah daga aiki kenan kafin ta tsari napep ta dawo gida kuma 2:30PM yayi. Tana shigowa gida Aiman dake carafke tsakar gida tasoma mata “Oyoyo Ya Fannah” cewar Aiman dake da shekara 8 kenan baki kam masha Allah. “Oyoyo Aiman” cewar Fannah tare da hugging nata. “Ina sweet d’ina Ya Fannah?” “Laaa kinga yau na mance ban siyo miki ba in shaa Allah zan siyo miki gobe, yi hak’uri kinji?” “Ai dama haka kike cewa kullum inda saurayin kine ai baraki mance ba.” Cewar Aiman tana guna-guni. “Ya SALAM!!!” Fannah ta zaro ido “ban hanaki maGanan saurayi ba? Ni narasa ina kikejin wanga zance.” “Sekin tambaya ne Ya Fannah?” cewar Afrah data fito daga d’aki “wannan maras kunyan kuma.” “Ai wallahi Ya Afrah ko kiyi shiru ko in fad’awa Ya Fannah batun wancan saurayin dayazo wajen ki d’azu da Mami batta gida.” Kai Afrah ta dafe “banza! ai kin riga kin fad’a matan kuma wallahi kisani baran sake baki chocolates ba in yakawo min.” “Wait wait wait Afrah saurayi kika soma kawo wa gida bada sani na ba?” Cewar Fannah in a serious tone. “Ya Afrah fa ba saurayi na bane munafircin wannan munafukan ne, Ibrahim nefa classmate d’ina na secondary school.” “Meaning? Afrah bawai zan hanaki yin samari bane kawai becareful karki yarda da maza so easily zasu kaiki ne su baro ki.” “In shaa Allah ya Fannah I'm very vigilant.” _6 hours later..._ Mami da su Fannah ne zaune a d’akinsu suna d’an tab’a hira. “Fannah nace wannan karan se ankai har k’ashen wata za’a biyaku?” “Eh Mami” ta amsa da fara’arta “wani abu ne?” “Fannah Habibti nasan kina mana sosai in ba ke family'n nan would have been dead by now, mungode sosai Allah cigaba da miki bud’i ya miki albarka kuma.” “Ameen Mami dan Allah kidena min godiya, you guys deserve all that I'm doing for you. We are family. Kina buk’atan kud’i ne? Kaman nawa?” “San samu dubu biyu kinga Maman-” Katseta Fannah tayi “a’a Mami ba sekin min bayanin me zakiyi da kud’in ba” nan ta ciro wallet nata ta irga N4000 gashi jiya mun samu ankai mu wani meeting da akayi na commissoners so anbiya mu kud’i. “Nan N4000 gashi zdmiki aiko?” “Fannah N2000 ma ya isheni dan Allah ki rik’e sauran kema kinada buk’atunki ai.” “Mami dan Allah ki amshi ai ni na baki.” Hannun Mami tabud’e tasa mata kud’in ciki. “Nagode Habibti Allah miki albarka yakuma k’ara bud’i.” “Ameen Mami nagode da addu’arki Jazakillahu khairan. Barinyi sallah in kwanta k’arfe bakwai zan fita gobe akoi meeting da za’ayi muzamuje muyi serving abinci can.” “Toh ki huta gajiya nima barinje in samu Babanku. Seda safe.” A tare Afrah da Aiman da Fannah duk sukace “Allah bamu alheri” sannan Mami tafice bayan ta amsa da “Ameen karku manta kuyi addu’a” Ya Fannah zan d’an samu d’ari biyun kati ne? Cewar Afrah tana b’oye fuskarta. ‘Yar murmushi Fannah tayi “saboda kisamu na kiran samari ba” “Haba! Dan Allah Ya Fannah wallahi a’a.” “Toh Allah kaimu gobe zan baki, kwanan nan bana spending much muku kuyi hak’uri tara kud’in nake ne Afrah inason kai Baba asibiti kinde san ya jikin nasa yake.” Kai Afrah ta giad’a alaman tasani sosai. “Mun gode sosai Ya Fannah Allah k’ara bud’i.” Da amsar “Ameen” suka kashe wuta suka kwanta. ★★★★ *ANAS* Sosai Anas ya k’ara kyau, fari da fresh, shekaru sun k’aru yazama cikakken saurayi yanzu me shekaru ashirin da uki (23) a duniya. Jikinsa muscular yake, packs nasa na nan guda hud’u dadai ba guda shida irin na wrestlers ba. Tsayayyen na miji yake yad’an k’ara kauri kad’an kan sirancinsa wanda yasake fito da kyansa. Sede kam hali na nan na shaye shaye dukda cewar har a yau Abuu da Ummie basu san yanayi ba, duk wanda yaji ance Anas na shaye shaye ma bare yarda ba saboda erin hankalin dayake nuna wa mutane, kominsa a b’oye yake. A da se in yayi mafarkin Ummimi ko na yarinyan dayayi raing yake sha amman banda yanzu, haka kawai in ya rasa abin yi ze kurb’a abinsa. Allah shirya. A wannan shekaran yagama makarantarsa na London. Tun tafiyarsa be dawo gida ba sanda ya k’are shekaru biyar d’in cur! Cikin ikon Allah kuwa yafito da excellent result, school nasu sunyi dashi ya soma musu aiki dan iya zanen Anas as an architecture amman sam yak’i saboda san cika burinsa na karya wa mata zuqatansu, yafisan yayi da matan Nigeria kaman sa ba tsinannun turawa ba. Amal tasa ta girma sosai shekarunta 13 yanzu, ba abinda ya rabata da Anas kyau kawai ya d’ara ta da kad’an. Amal an d’an soma wayo amman har yanzu halin autan ta nanan dakuma rashin kunya da rashin shiri da Shettima. Shettima har yau besan ya girma ba shekarunsa ishirin da d’aya da abu a ka amman hakan be hanasa papiro Fannah da gudu in tamasa rashin kunya. Cat and dog Ummie ke ce musu. Anas kuwa saide in bai gida sarai fa yasan Amal ce da laifi amman haka zebata gaskia yabawa Shettima laifi se in sun keb’e yake basa hak’uri. Sosai Anas yaya ne me hankali, yana kula da k’annansa ba kamar da ba kuma yanzu in yana cikin family’nsa yana murmushi da walwala sosai seda Amal ne kawai yake dariyan da har za’a ga fararen hak’waransa tas. Su Baana da Kashim ma suna nan sun bud’e ‘yar sana’a tare and alhamdulilah Allah na sa musu albarka. Shettina kuwa yasa san jiki a gaba, sam bayasan yin abu wa kansa yayi depending da Abuu kawai ‘cause yanzu masha Allah Abuu arziki se bunk’asa yake tunanin komawa Maiduguri ma yake sede har yanzu nothing is certain yet. A yanzu haka Anas yana garin Maiduguri yazo neman aiki kwanansa uku kenan yau yakeda shirin fara fita neman aikin, Allah bada sa’a. Construction industries yasoma bi sede yawancin su se suce basu d’iban masu aiki yanzu ya dawo bayan wasu ‘yan watanni dukda kyan result nasa kuwa haka ya gama yawo a ranar farko besamu aiki ba. Ranar biyu ma haka ya jera kusan sati yana neman aiki kap babu har yayi giving up kan monday ze koma Bama ze huta yanzu a weekends a gidan chairman daya sauk’a. Yana kwance a guest room kan gado Iphone nasa yayi ringing yana kai dubansa yaga “My angel” Amal kenan. Da murmushi kan fuskarsa ya d’auka. “My Angel” ya fad’i. “Na’am Ya Anas d’ina ina wuni?” “Lafiya qalau Angel ya kike ya school?” “Lafya qalau Ya Anas, yaushe zaka dawo baka samu aikin bane har yanzu?” “Ban samu ba Angel ina kan nema har yanzu amman nakega monday zan dawo. Kinasani cikin addu’a ko Angel?” “Sosai Ya Anas yanzu ma dana idar da sallah sanda nasaka ciki” “Yawwa My Angel ya Ummie toh?” “Lafiyarta qalau. Ya Anas kaga Ya shettima d’azu ya mareni.” Ta fad’i kamar zatayi kuka. Yana kishingid’e jin Amal tace Shettima ya bugeta yasa ya zauna tare da zaro blue eyes nasa. “Ya mareki? A dalilin meh?” “Wallahi ba abinda na masa Ya Anas kawai fa abokansa ne sukazo yace in gaishesu nikuma nak’i saboda hak’ori na na ciwo shine bayan da suka tafi ya mareni a bayana wajen har yayi pink.” Sarai yasan Amal da rashin kunya daga ji ba k’in gaishe da abokan nasa kad’ai tayi ba in aka bibiya halan har zaginsu ma tayi. “Toh yi hak’uri Angel yanzu zan kirasa in sissilesa na dawo kuma zan rama miki.” “Yawwa Ya Anas ba-bye.” Ding! Ta kashe. Komawa yayi ya kwanta tare da zira wa ceiling ido yana murmushi wa kansa daidai lokacin wayarsa tayi k’ara yana kai dubansa yaga number ke kira, zurawa screen d’in ido yayi yana nazarin wacece can yace wannan number Meenor ce. Sanda ya kusa tsinkewa sannan ya d’aga batare da yace komi ba wata murya ce me zak’in gaske ta soma magana a hnakali dukda cewar cikin tashin hankali kuwa take. “Haba dan Allah blue eyes, menayi kuma wannan karan? Tun jiya nake ta trying number’nka sarai kana gani ignoring d’ina kawai kake.” “Toh nayi, zaki iya yin wani abu ne?” Gatsau ya bata amsa. “A’a dan Allah blue eyes kar muyi haka dakai I'm sorry, I love you.” “Meenor nomore of that we are done, karki sake kira na please ko kin kira ma barin d’auka ba.” Karap ya katse wayar. Kafin ya ajiye ta soma kira again sa number’n nata yayi a call divert tare da sakar da murmushi hakwaran samansa suka bayyana. “7 of 100 kenan.” ya cize light red lips nasa. Ma’ana cikin mata d’ari daya d’au alwashin ze kariya masu zuciya yaci nasara kan guda 7 wannan ma tun kafin yasamu aiki yazama billonaire kenan! *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:46, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 1⃣4⃣ “Hello Abuu?” Cewar Anas ta waya. “Anas Baba na ya kake?” “Lafiya Abuu I have a suprise for you” “Toh inaji Baba na.” “Nasamu aiki!” Anas yayi exclaiming. “Ahh toh Alhamdulillah a ina haka?” “A Flames Enterprises Abuu, kuma as Personal Assistance na CEO’n wajen.” “Wai wai! Kana nufin Alhaji Muh’d Muh’d??” Abuu ya tambaya cike da mamaki. “Shi Abuu salary na N500,000 da weekly allowances N5000.” “Kai Baba na namaka murna barin fad’awa Ummie se add’ua take ta maka.” “A’a bari Abuu I’ll call her dakaina banasan Amal tasan she is not the first person I called to tell.” “Uh!” Abuu yayi exclaiming “kai da wannan ‘yar takan.” Murmushi Anas yayi “Aikam Abuu ina karb’an first salary na shopping zankai Amal.” “Toh Allah maka albarka Anas yacigabada bud’i congratulations.” “Thank you Abuu se mun sake magana.” “So yanzu zaka shigo Monday d’in still?” “Eh zan shigo saboda in d’iba kayakina I have untill next week inyi resuming office.” “Okay toh yayi kyau, welldone.” Ahaka sukayi sallama. Anas na cikin searching contact na Amal wayarsa ta soma k’ara number ke kira bayan yad’an zura wa number’n ido ya gano Teema ce. Murmushi yayi sannan ya d’aga batare da yace komi ba. “Hello angelic blue eyes” cewar budurwar. “Yes” ya amsa ba tare da ya nuna damuwa ba. “Blue eyes fad’a muke ne? Tun jiya nake expecting call naka shiru.” “I have far worth important stuffs to attend to than you Teema.” Har tsakiyar kanta ta jiwo wannan zagi amman ta danne zuciyarta. “Blue eyes dama so nake in sani ko you are free zuwa anjima da yamma inason mu fita ne, like a date.” “What are you implying Teema? Kina nufin ni bansan abinda yakamata ba se kece zaki bani time da zamu fita date dake?” Ya fad’a a tsawace. “Blue eyes please calm down ba abinda nake nufi ba kenan naji kace gobe zaka koma Bama I want to spend some time with you kafin ka tafi.” “Huh!” Ya saki numfashi. Tare da jawo kad’an daga cikin gashin kansa yana wasa dashi da wata mirmushin mugunta a fuakarsa. “Nikuma banaso kinsan me Teema? Lets just end it bana sonki anymore lets break up, we are done karki sake kira na ko kin kira barin d’auka ba.” “Blue ey-” bata k’are maganar ba ya katse nan take ta sake kira kalan abinda yama Meeno ya mata. 8 of 100 ya murmusa sosai wanda ya mugun k’ara masa kyau. Amal nasa ya kira ya fad’a mata yasamu aiki. Tsalle ta riga dakawa haka suka sha hira sannan yace ta kai wa Ummie wayar. Sosai Ummie ta masa. Shettima ne k’arshe ya kira ya fad’a masa aikin daya samu, sosai Shettima uwar san jiki yamasa murna at long last ze soma jin dad’i dan yasan halin Anas be iya rowa ba inba wai dagangan zeyi ba, mutum ne me kyauta amman fa ma wanda yaga dama. ★★★★ Da misalin k’arfe 3:30PM Fannah ta dawo gida da ledoji manya manya hannunta siyayya tama family’nta sosai. Mami, Afrah da Aiman duk suna tsaye tsakar gida hankali tashe a tunaninsu ko wani abu ne yasamu Fannah saboda duk sanda zata wani waje daga gun aiki tana kiran Mami ta sanarda ita wanda yau batayi ba. Tana shigowa Mami tayi kanta tare da rungomata “Fannah ina kikaje? You made us worried sick gashi nata kiran wayarki akashe.” “Wallahi game natayi seta mutu, kubar tada hankalinku please in shaa Allah ba abinda ze sameni. Kasuwa na wuce nad’an mana siyayya.” Nan Afrah da Aiman suka k’ariso tare da karb’an ledojin akan tabarma suka zauna tare da zazzage kayakin. Kitchen utensils ne, food items, seda sweets da chocolates dakuma atamfofi guda hud’u masu kyan gaske seda shadda guda biyu, se sauran k’ananun abubuwa irinsu tissue, toothpick da sauransu. “Fannah ina kika samu kud’i haka ko har anbiyaku albashin ne?” “Ko kad’an Mami, ina meeting dana fad’a muku za’a kaimu serving d’insu yau?” Mami ta giad’a kai “ashe harda Alhaji Muh’d Muh’d CEO’n Flames Enterprises.” “Haba keh!” Cewar Mami. “Ya Fannah kap Maiduguri fa ba wanda yakaisa kud’i!” Cewar Afrah. “Ya Afrah shine wanda muke gani a NEWS yawancin kullum?” Aiman ta tambayi Afrah. “Eh shi” Afrah ta amsa ta a takaice. “Toh shida d’ansa sukaje ni akace na kaimusu drinks nasu bayan nakai nakega se d’an nasa yace baya shan flavour’n drink d’in baban nasa ya kirani na canzo masa nazo tafiya kawai Alhj Muh’d d’in ya kirani ya mik’a min bandir na N500 kyauta bayan da aka k’are meeting d’inkuma da muka raba kud’in da aka bamu na tashi da dubu goma albashi na na wata fa kenan ga kuma dubu hamsin. Daga can na wuce kasuwa namana d’an siyayya dududu kayan dubu talatin ne anan.” Aiman mathematician har an buga lisafi “sauran miki N30,000 kenan.” Kallonta Fannah tayi tana murmushi “welldone ashe surutun nan naki ba’a banza bane tunda kin iya math haka.” “Math d’in ‘yan primary three ba” cewar Afrah tana duba zannuwan. Aiman zatayi magana Afrah tace, “Ya Fannah wannan zannuwa fah?” “Namu ne biyu na Mami ta zab’a ciki, guda biyu iri d’ayan kuma naki da Aiman.” “Haba Ya Fannah mena siya min turmin zani iri d’aya da wannan maras kunyan.” “Yo! Ked’inma ance miki inasan yin anko dake ne? Ya Fannah mungode sede har yanzu banga sweet d’ina ba.” Cewar Aiman. Nan Fannah ta bud’o jakarta ta ciro packet na sweet “ungo wannan duka naki ne kika rabawa ‘yan ajinku kuma ni ba ruwa na.” Amsa tayi tana tsalle “nagode Ya Fannah ai ko Ya Afrah ma barin bata bale ‘yan ajinmu masu kwad’ayin nan, wallahi Falmatan nan har k’wai na sanda taci ranan” Zani biyu iri d’ayan ta d’au d’aya tashige d’akinsu dashi. “Ke dawo nan waya ce miki ki d’auka?” cewar Afrah jan d’ayan tayi itama ta ruga tabi Aiman cat and dog kenan. “Fannah Allah miki albarka, Allah k’ara miki bud’i yaci gaba da kare mana ke. Mungode matuk’a da d’awainiyan da kike mana dukda kuwa ba responsibility’nki bane wannan aiki na ne da Babanku amman kinayi. Kiyi hak’uri.” Hannun ta Fannah ta rik’e bibbiyu cikin nata “Ameen nagode da addu’arki Mami amman dan Allah kidena min godiya ba godiya tsakani na daku Mami. Na ware dubu ishirin cikin kud’in gobe seki kai Baba asibiti a duba shi ko magani a basa tunda baramu iya affording aikin da za’a masa ba.” “Toh Fannah, sannu da k’ok’ari Allah miki albarka.” “Ameen” tace “barin je in samu su Afrah ciki, ki d’au zannuwa biyu anan shaddojin kuma na Baba ne.” “Toh mungode sannu.” Fannah na shigowa d’aki tasamu Afrah da Aiman se dambe suka dak’yar ta rabasu zani de gasu iri d’aya amman ahakan ma se anyi fad’a. Bayan ta rabasu ta kori Aiman dawayo in bahaka ba sun hau wasan habaici kenan. Ana kawo wuta ta had’a wayarta a charging. Kayakinta na cikin wardrobe take shiryawa a yayinda Afrah ke kishingid’e kan gado tana game a wayarta. Can ta nisanta sannan takira Fannah. “Ya Fannah!” “Na’am Ya Afrah, mene kuma yanzu?” cewar Fannah tana ninke kayakinta. “Kikace d’azu kinga Alhaji Muh’d Muh’d?” Kai Fannah ta giad’a batare da ta kalleta ba. “Okay da d’ansa kuma kikace sukaje wajen?” Afrah ta fad’i kalma d’ai d’ai. Barin abinda takeyi tayi ta juyo ta kallon Afrah “what are you implying?” D’an dariya Afrah tayi “guilty concious?? Ni bance komi ba kawai cewa nayi kinga d’an Alhj Muh’d?” “Nope ni bangansa ba.” Fannah tabata takaicaccen amsa. “Wow! Yau me hana mutane k’arya keyi? Hilarious.” Cewar Afrah tana mocking smile. “Kuma se akace miki k’arya nake. Allah ban ga d’an nasa ba.” “Toh ikon Allah kuma ke fa ke kika kai musu drinks nasu? Kodan had’ewarsa yasa baki gansa ba?” “Ke wallahi Afrah suratan banza sun miki yawa. Ni ko zaki samin wuk’a a wuya bansan kalar fatar sa bama bale insan ko kyakkyawa ne ko mumuna. Muryarsa kawai naji.” “Haba!” Afrah ta daka tsalle tare da baro inda take ta matso kusa da Fannah. “Ya muryar tasa take Ya Fannah? Fad’amin please kinsan su yaran masu kud’i muryarsu ma daban take.” Shiru Fannah tayi tana nazarin muryar Anas dasuka d’au d’an Alhj Muh’d ne. “Well ba hassada muryarsa nada zak’i irin zak’i ta mazan nan and yana cracking hakan nan. Barin miki bayanin yadda zaki gane kinsan muryar Lancelot nacikin season film Merlin ba?” Kai Afrah ta giad’a sau uku. “Toh haka murayarsa take sede kamar zatafi na wancan d’inma dad’i. Toh kinji, matsa min nacigaba da abin dake gabana.” “Iyye! Har kinsa na fara imagining wannan d’an billonaire nasan definately zeyi kyau sesa hakan ma ba’a nuna sa a NEWS gudun kar ‘yan mata su bisa.” Kallo Fannah ta bita dashi “kefa wallahi surutun banzanki sunyi yawa.” “Hummm! Afrah taja numfashi “Ya Fannah kenan. Kinsan muryarsa meaning kunyi magana kenan.” “Wai meke damunki bamuyi magana ba acewarki yaran da ubansu billonaire suna magana wa mutane anyhow ne? Ko kallona ma beyi ba dana ajiye masa drink d’in kamar yadda nima ban kallesa ba thank you kawai naji yace.” “Iyye! Amman daya miki magana fa? Zaki amsa?” “Ke qaniyarki, Afrah kika sake maganan wancan saurauyin bake ba kud’in kati se next month.” Tsit Afrah tayi bata kuma cewa komi ba, ahaka Fannah tasamu tagama had’a kayakinta cikin wardrobe. _One week later..._ Anas ne tsaye gaban dressing mirror a d’akin da chairman yabasa. Yau ze soma zuwa office he is feeling nervous sosai. Sanye yake da mint blue shirt me long sleeves da cufflinks, seda jean trousers. Simple shiri ne amman yamugun amsar sa he is looking way smart. Jakar laptop nasa ya d’ago yasa laptop d’in ciki da sauran takardu kad’an sannan yasake kallon kansa jikin madubin sannan ya fice bayan ya karya ya wuce office. Yana isa gaban building d’in da za’a iya kira da mini sky scrapper ya tsaya. A k’alla floors za suyi 7-8, dogon gini ne sosai wanda jikin bangon yake glass. Building ne babba bakin k’ofar an rubuta FLAMES in caps. Wani button ya danna k’ofar glass d’in ya bud’u yana shiga k’ofar yayi scanning nasa bayan ya tabbatar baya d’auke da makami sannan wata k’ofar ta sake bud’uwa nan ne mutanen cikin ginin suka bayyana. Maza da mata kowa se aikin gabansa yake very organised. Wajen shiru ba hayaniya. Wajen dayaga an rubuta RECEPTION ya k’arisa mace ce tsaye wajen gabanta telephone ne da pack na pencil da biro seda files kuma. Tun kafin ya mata magana tace dashi “Hi” tana washe 32 inta acewarta taga bature. “Hello” ya gaisheta back, “erm I want you to direct me to Mr. Muhd’s office, the CEO.” “Okay American's most handsome” tace dashi. “Whats your name?” “Anas Ibrahim Fauzy.” Ya amsata a takaice. Baki tasake wangalau wai dama ba bature bane? “Excuse me, I mean your name. Name.” dan bata yarda muslimi bane. “Yes Anas Ibrahim Fauzy. Ko kema kin d’au Joseph ko Andrew ne sunan nawa? My name is Anas for goodness sake.” ya fad’a a tsawace. “I'm sorry blue eyes” ta fad’a tare da kashe masa ido. Tsuka yaja tare da kawar da idanunsa daga kanta. “Uhm are you two having an appointment with the CEO yasan da zuwanka?” “What nonsense? Da inbe san da zuwa na ba zanzo nan ne? Take me to your CEO” yayi demanding ba alaman dariya a tatare da fuskarsa. “Mesa yawancin kyawawan mutane basuda hali ne?” Cewar receptionist d’in a hankali aikuwa Anas ya jiyota harara ya watsa mata bayan d’an dube-duben da tayi a system dake gabanta tace, “I'm sorry Mr. Fauzy seems like ba sunanka acikin wad’ana zasu ga Mr. Muh’d yau maybe next time.” “Kinsan wani abu? Tunda nake a duniya ban tab’a ganin senseless mutum kamar ki ba.” Dadai lokacin elavator ya bud’u Mr. Muh’d ya fito daga ciki. Taku d’ad’ai kamar yadda ya saba yayi yatako zuwa gabansu Anas cike da girmamawa Anas ya gaishesa. “Ya Anas me kakeyi baka shigo ba har yanzu? I've been waiting for you” “Baba wannan receptionist d’ince ta rik’eni wai baran shiga ganinka ba.” “No Sir ba hak-” Katse ta Mr. Muh’d yayi rai a b’ace “this should be the last time da zaki sake hanasa shigowa nan he is Anas my son, copy that!” ya daka mata tsawa. “Yy..yyess sir, my aplologies please.” “You apologise to him not me.” Kallon Anas take yana mata murmushin mugunta, “Mr. Fauzy I'm sorry.” Harara ya watsa mata sannan yace, “apology accepted.” Nan Mr. Muh’d yaja hannunsa “come lets go in nuna maka office naka.” A floor na k’arshe yakai Anas inda aka rubuta *Mr. Fauzy* a bakin k’ofar d’akin. Office ne babba da split AC ciki, office kujeru ne manya guda biyu da table d’aya. Akoi telephone da flat screen desktop kan table d’in seda notepad, da pen dakuma pencil pack. Gefe guda kuwa fridge ne seda plasma TV. “This is your office, inda abinda be maka ba let me know se a giara” Godiya sosai Anas ya masa tun daga ranan Anas ya soma aiki. He is very punctual, duk meetings da schedule na Mr. Muh’d shi yake maganing. Kasancewar duk Enterprise d’in ba architecture’n daya kai Anas iya zane, duk sanda za’ayi zanen project Anas keyi, wannan kenan! *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:46, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 1⃣6⃣ *ASSALAMU ALAIKUM MASU KARATU, INASON INYI AMFANI DA WANNAN DAMA IN FAHIMTAR DA MASU K’ORAFI KAN LITTAFI NA, NACEWA INA YAWAN SA TURANCI CIKI. RIGHT FROM THE START NASO DAMA IN YI MAKING IT CLEAR KAN ZA KUNA YAWAITA GANIN TURANCI CIKIN LITTAFIN NAN AMMAN KUMA SENA FASA. GANIN ANASON A MAIDA ABIN SUBJECT OF DISCUSSION YAZAMA DOLE INYI MAKING IT CLEAR YANZU. IN KUKA LURA BAWAI NA K’WARE A HAUSAN BANE, KOYO NAKE HAR YANZU, BA BAHAUSHIYA CE NIBA ‘YAR MAIDUGURI CENI, YOU GUYS KNOW RIGHT ‘YAN MAIDUGURI BA’A SASU CIKIN JERIN HAUSAWA. INDA NA K’WARAI A HAUSAN AI BARIN NA SIRKAWA DA TURANCI BA. KUGANE PLEASE KUNA MIN UZURI. MOREOVER, A CHAPTER’N BAYA CHAPTER 15 KENAN, NAGA SHINE NASA TURANCI SOSAI SABODA A OFFICE SUKE, SANIN KANKU NE MASU K’ORAFI BA’A CIKA YIN HAUSA A OFFICE BA, ENGLISH UNIVERSAL LANGUAGE AKE SPEAKING. INA FATAN DAGA YAU MUNYI SOLVING WANNAN ISSUE. THANK YOU SO MUCH, I LOVE YOU GUYS HAVE FUN READING!!!* Ba tare da ya kalleta ko yace da ita komi ba yacigaba da abinda yakeyi cikin laptop dake gabansa. Tafi minti biyu tsaye sannan ya ciro wata paper daga drawer ya ajiye kan table d’in. “Here is the coffee description, sugar should be minimum.” K’arisowa tayi ta d’aga paper’n lallai ma d’an wannan order’n ne bare irga min ta waya ba seya sa nazo all the way here. “Sir is that all? Naga ai irin wannan orders muna d’aukawa ta waya.” Ba tare da ya kalleta ba daka tsawa “just shut up and leave please!” Har tsakiyar kanta tajiyo wannan tsawa rabuwanta da a daka mata tsawa haka tun barinsu Bama. Take tajiyo hawaye na ciko wa idanta daman ita ba me daure masifa bane, batare da tace komi ba tajuya ta kama tafiya tana share hawayenta nan ne ya d’ago kai yana kallon bayanta har ta bud’e k’ofar ta fice. Da misalin k’arfe 3:50PM su Fannah suka iso conference hall d’in komai is in place. 4 on the dot su Anas suka hallaro hall d’in. Fannah na ganin sun shigo ta fice ko sa Anas a ido batai ba, bata masan wani kalan kaya yake sake da ba, se sanda za su soma serving coffee’n ne ta dawo kanta a k’asa take tafiya dan karta jawo attention, haka table by table take bi tana ajiye coffee’n. Table nasu Anas takai k’arshe a hankali ta d’aga kai dan sasa a ido saidai ba direction nata yake kallo ba ya juya yana magana da d’aya daga cikin mutanen kan table nasun. K’eyarsa kawai tagani yadda yayi styling gashin kansa me tsawo wane na bature. Bayan ta gama ajiye musu tajuya zata tafi kenan taji familiar voice ya kirata da “waitress” gam ta rufe idanta a hankali ta juya “yes sir” lokacin kuma Anas ya juya yana magana da wasu, k’arisawa tayi ta tsaya daga gefensa “yes sir!” Ba tare da ya kalleta ba yace, “take this away I don’t take coffee.” Kallo ta k’are masa sannan ta d’aga ta fice. Mamaki ne yacika ta wai waye wannan Anas ne ko me sunan san yake feeling like. Bayan taron ya watse suka raba kud’in da suka samu sannan ta dawo gida d’aki ta wuce direct. Afrah tasamu se faman chatting take bayan ta mata sannu dazuwa seta karinci kamar wani abu na damun Fannah. “Ya Fannah lafiya?” “Wani irin lafiya? wallahi wannan d’an Alhj Muh’d d’in ji da kai ya masa yawa. Bakiji yadda yake ma mutum magana ba ke ko kallon mutum ba yayi.” “Kina nufin Anas Ibrahim Fauzi?” Cewar Afrah. “Eh wai haka naji sunan nasa amman ya akayi kika sani?” “Yanzun nan aka nuna sa a NEWS nake gama meeting d’inda kuka jen ne. Yasa black suit da white shirt da black necktie ko?” Cike da mamaki Fannah ke kallon Afrah. “Eh haka” ta amsa ta. “Ya Fannah baki ga kyansa ba wallahi kamar bature.” “Toh ai kyansa be amfana sa ba tunda baida hali me kyau.” “Ya Fannah waya keta hali? Ke bakiga fuskarsa bane?” “Bangani ba kuma bansan gani, ni mubar maganarsa ma he is so arrogant. Barinje inyi wanki kafin Maghrib yayi.” Wankin ta takeyi hankalinta kwance tajiyo kiran Afrah daga d’akinsu Baba. “Ya Fannah! Ya Fannah! kizo da sauri.” Nan ta bar abinda take ta ruga a guje ciki acewarta kowani abu ne yasami Afrar dan su Mami basu gida takai Baba asibiti Aiman ta rakata. “Afrah lafiya?” Ta bankad’o labulen d’akin zaune tasamu Afrah gaban TV “Ya Fannah gashi nan! Anas d’in” kafin Fannah ta kai dubanta kan TV’n har ya juya sede taga kamar ta ga fuskarsa kamar kuma bata gani ba. “Mstw tun d’azu nake kirar ki gashi ai har ya kau da kansa” “Yanzu Afrah fisabilillahi akan ganin wannan Anas d’in kika kirani all the way here nafa d’au ko wani abu ne ya same-” Bata k’are maganar ba Afrah da hankali ke kan TV tasomsa sabon ihun “gashi nan! gas-” karap NEPA suka d’auke wuta. “Oh damn it! NEPA bakuyi ba.” Tsuka Fannah taja sannan ta koma ta cigaba da aikin dake gabanta. _Wattani da dama sun shud’e..._ Rayuwa ta cigaba da kasance wa Fannah daidai ba abinda ya sake had’ata da Anas. Tana zuwa gun aikinta kullum. Baba kuwa magunan da aka basa a asibiti cikin ikon Allah yana samun sauk’i sosai. Tsoron Fannah d’aya ne rananda magunan zasu k’are bata san ina zata samu kud’i asake sai masa ba. Kullum cikin add’ua take. Ta b’angaren Anas kuwa abu sunan yadda suke shaye shaye dakuma breaking up da ‘yan mata kullum yana kan yi. Saidai ba kamar da ba, d’an watannin baya da suka wuce sam yadena mafarke mafarken daya saba na Ummimi da kuma yarinyar dayayi raping but kwanan nan sede be kwanta ba seyayi mafarkin yarinyan dayayi raping d’in wai ta dawo garesa. Syrup nasa yake kwankwad’a bayan kwana biyu yasake tashi da mafarkin ji yake yarinyan is somewhere close to him. To kode tana d’aya daga cikin ‘yan matan daya tab’a breaking up dasu ne? Kai! A’a da k’yar ai ita wancan a Bama take. To ina take?? Shettima dake tsaye a kansa ne yayi ihu dagangan dan tsoratar dashi. “OMG!” cewar Anas da hannu dafe kan k’irjinsa. “K’aniyanka kasan yadda kaban tsoro kuwa!” har yanzu nishinsa be dawo dadai ba. Dariya sosai Shettima ke “hahaha! Kaga fuskarka kuwa? Anyways tunanin me kake har na shigo d’akinka baka sani ba.” “Kajima anan ne?” Anas ya tambaya yana k’ok’arin daidaita numfashinsa. “Yup about 2 minutes ago” cewar Shettima. “Babu, ba tunanin da nakeyi.” “Oh common! Ya Anas kama dena min k’arya kasan ko lokacin da ka b’oye min lamarin abinda kama wancan yarinyar a Bama nagane so just tell me what is it now?” Tasowa yayi ya zauna, shima Shettiman ya zauna kusa da wansa “tell me ina jinka.” Nishi Anas yaja “kasan wani abu ne? Its been long banyi mafarkin wannan yarinya ba but yanzu anytime na kwanta tunanin ta kawai nake ji nake kamar *_TANA TARE DA NI_* I don’t know whats wrong kullum cikin tunaninta nake Shettima I can feel it yarinyar bata mutu ba.” “Toh fahhhh” cewar Shettima dan ko besan me zaice ma wansa ba he is speechless. “Fad’a min Shettima what are you thinking?” “Well, Anas maganar gaskia bansan me zan ce maka ba. Yarinyar nan fa a Bama take theres no way zata dawo Maiduguri kuma kai da bakinka kace she was 15 time da abin yafaru who knows ko bata rayu bama an-” Katse sa Anas yayi “No Shettima I can feel it, bata mutu ba” hannu yasa cikin gashinsa “I don’t know what to think anymore, inasan ganin yarinyar in nemi gafararta Shettima.” Kafad’arsa Shettima ya dafa “komai will turn out perfect karka damu, wayasani ko ta kasance d’aya daga cikin ‘yan matan da kake wasa dasu. Saboda baka san fuskarta ba.” “But I’m sure ita tasan nawa ai, in ta ganni zata gane ni tunda ita ba’a buge take ba time d’in.” “Tsab ko zata iya mancewa da fuskarka Ya Anas, katuna da dare ne ranan kuma ruwa akeyi, in har ta rikice beyond imagination alokacin sosai tsab zata mance da kaman ninka. Allah desa bata kasance d’aya daga cikinsu ba.” “Ameen” Anas yace sannan ya koma ya kwanta tare da zura wa ceiling ido. Wayarsa ya soma k’ara yana kai dubansa yaga family doctor’nsu ne, ba tare da b’ata lokaci ba ya d’aga “Hello Dr Mansur?” “Hello Anas kabar duk abinda kakeyi kazo gidan Babanka yanzu.” ya fad’i cike da tashin hankali sannan karap ya katse wayar. “Hello..? Hello...?” Zabura yayi yajawo jacket nasa yasa tare da d’auko key’n motarsa ya fice a 360. Bayan ‘yan mintuna ya iso gidan Mr. Muh’d. Sama ya haura direct zuwa d’akin Mr. Muh’d can yasamu Dr Mansur tsaye a bakin k’ofar. “Dr Mansur whats wrong? Meya samu Baba?” “Anas is about time kasan gaskiya Babanka yata b’oye ma gaskia saboda bayasan ya saka cikin tashin hankali amman yanzu da lokaci yariga ya k’ure I have to tell you.” Take idanun Anas ya cike da hawaye “meke faruwa Dr. Mansur? Meya samu Baba?” ya tambaya murya na rawa. “Anas calm down tunba yau ba Baba ke suffering da cutar cancer.” “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un” Anas ya saki salati. “No thats not true please karka ce haka Baba baida cancer.” Kuka yasoma yi sosai. “Anas thats why nace maka you need to calm down yanzu ba lokacin musu ko kuka bane addu’a zaka masa. Kasan shi matsalar cancer ba’a cika discovering na sa da wuri ba bale ayi maganinsa saboda bai da symptoms cin jiki yake sosai the moment ya kama mutum. Haka yasamu Baba ma, yau shekara kenan yana fama da cutar a iya sani na kenan. Duk sanda kaji Baba yace maka zeyi tafiya to ciwon nasa ne yatashi.” “Dr Mansur niba wannan ba dan Allah” yasa hannu ya share hawayensa. “Do something to save him please.” “I’m so sorry Anas but its too late, saisa nace maka addu’a zamu masa yanzu lokackin Baba yayi, be a man please, kai kad’ai Mr. Muh’d keda bayida wani family bayan kai, you have to be strong.” Inaaa Anas se kuka sun shak’u da Baba sosai wane Abuu. Kuka yake sosai Dr. Mansur na basa hak’uri ganin ba mahillici se Allah yasa ya share hawayen sa a hankali ya bud’e k’ofar d’akin Mr. Muh’d. Kwance yagansa rai a hanun Allah wani kukan yasake faso masa jiki a sanyaye ya k’arisa gaban gadon nasa ya tsuguna tare da rik’o hannunsa yana kuka. “Baba dan Allah kar ka tafi kabarni, kar ka tafi kabar Enterprise naka we need you.” Magana ciki ciki Baba yace, “shhh Anas, bar kuka ni zan tafi amman na bar musu kai. Kai na mallakawa Enterprise d’ina da duk wani abinda na mallaka” “Noo... Nooo please Baba” Anas ya katse sa. Baba yacigaba “na riga nayi signing komai under your name Anas, kamar yadda nasan ka da hankali da hardworking ka cigaba da kula da Enterprise d’in koda a bayan raina, naka ne yanzu banida ikon in fad’a maka abinda zakayi dashi, just do what is right. Ban samu naga su Abuu da Amal ba tell them am sorry.” “Baba please kabar magana haka in shaa Allah zaka tashi baraka mutu ba please.” Wani irin numfashi Baba yasoma yi da k’arfin gaske. Gamgam Anas ya rik’e hannunsa yana ihu “No! No! Baba dan Allah karka tafi Dr. Mansur! Dr. Mansur!” a guje Dr. Mansur ya shigo saidai shima ba abinda ze iya tsayawa yayi daga gefe d’aya yana kallon yadda Baba ke nishi. “Dr. Mansur do something to save him please karka bari ya mutu.” “Anas I'm so sorry amman ba abinda zan iya masa, lokacinsa ne yayi.” “La ila ha illallah muhammadur-rasulillah salla-” be k’are ba numfashinsa ya yanke kap. Ihu Anas ya k’urma “Noooooo! Baba you can’t die please” hugging Baba yayi yana kuka yana jijjik’asa Dr. Mansur ne yazo yana k’ok’arin d’aga sa daga jikin gawan Baba amman ya kasa haka ya zuba wa Anas yana kukan cire rai yana basa hak’uri. Sun musan minti talatin sannan Anas ya tashi a garin yin haka wayarsa ta fad’i kasa “Ina zakaje Anas?” Cewar Dr. Mansur. Idanunsa sunyi jazir wane barkono blue eyes nasa sun k’ara shiga. Batare da ya kalle sa koya ce dashi komi ba yafice be tsaya ko inaba se bar (gidan giya) inda yaje ya bugun buguwa. He can’t take it mesa Baba ze mutu ya barsa? Wayarsa Dr. Mansur ya d’aga ya kira Abuu ya sanar dashi halin da ake ciki salati kawai kukeji. Bayan ya ajiye wayar ya rufe gawan Baba sannan ya fito a ranan aka ma Baba wanka aka sallace sa aka bisine sa. Kuka sosai kowa yake, ‘yan Maiduguri sun mugun jin mtuwan Mr. Muh’d. NEWS na ranan kap Mr. Muh’d aka yini ana nunawa. Ba inda ba’a nemi Anas ba an rasa ina yashiga se Allah, gashi wayar sa bata gunsa. Ranar de ta kasance a very bad day wa mutanen Maiduguri all in all. Se washegari da safe Anas ya dawo gida Allah yaso daya dawo Abuu da Ummie basu nan Shettima kad’ai a gida shi ya kula da Anas. Sosai Anas ya bugu ko d’aga k’afa bai iyawa Allah kad’ai yasan ya yadawo gida lafiya. Bayan Shettima ya tayasa rage kayan jikinsa ya kwantar dashi tare da rufe sa da bargo. Bacci sosai Anas yayi se shabiyun rana ya tashi. Shettima yagani zaune a gefensa yana karatu. Kansa ya rik’e yana k’ok’arin zama. Nan ne Shettima ya jiyo ya kallesa cike da tausayi. “How are you feeling Ya Anas?” Kallonsa kawai yayi ba tare da ya amsa sa ba. “Ya Anas hak’uri zakayi Baba lokaci yayi, zuwa gidan giya ka bugu is not a solution. Ba abinda ze amfanar da Baba kamar yadda bare amfanar dakai ba kaima. Addu’a ya kamata ka masa.” “No Shettima bara ka gane ba, baraka tab’a ganewa ba. Why is my life always like this? Se lokacin dana soma jin dad’i Baba ze tafi ya barni da burden na Enterprise nasa. Baran iya ba Shettima I can’t manage his company.” A hankali ya soma kuka kamar d’an yaro. *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:46, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 1⃣7⃣ “Oh common please Ya Anas, kowa yasan how you must be feeling, hak’uri zakayi ka d’au wannan ma wata k’addara ce.” Cewar Shettima yana shafa bayan Anas dake kuka. Daidai lokacin su Abuu da Ummie da Amal suka shigo kan gadon Anas Amal tayi. Ganin wanta na kuka itama tuni ta fara “Ya Anas bar kuka kaji? In shaa Allah Baba is in a better place yanzu.” Rungumosa tayi yana kuka ajikinta kamar d’an yaro. “Anas hak’uri zakayi, munsan yadda kaji mutuwan Alhj Muh’d amman yazama dole kayi tawakalli ga Allah kayi masa addu’a lokaci ne yayi. Yabar duk wani prperty’nsa maka inda hali zuwa anjima ‘yan jaridu sunasan magana dakai dangane da faruwar wannan abu.” “Noo Abuu please, ni baran iya kula da enterprise na Baba ba baran iya ba, kabawa ‘yan press hak’uri baran samu zuwa ba. Ni Enterprise nasan ma baran iya handling ba, I can’t.” Ya sake fashewa da kuka. Ummie ce ta k’ariso ta karb’esa a hannun Amal, “yes you can Anas, zaka iya. Babanka bare ji dad’i ba inda ze dawo yanzu yaji abinda kake cewa, ya bar maka company’nsa ne saboda ya yarda da kai da abilities naka, he is sure zaka iya cigaba da gudanar da lafiyar conpany’n saisa yabaka karka basa kunya Baba na. Kayi hak’uri kukan nan baida amfani gacan abinci na had’aka maka kaci kaje mutanen suna jiranka a TV station ko muce suzo ne?.” Kai ya kad’a yana kuka sosai. Bayi ya fad’a dan yin wanka amman wankan ma yakasa damuwa sun masa yawa shower kawai ya kunna ruwan nata zuba kansa kusan na minti ishirin sannan yafito yasa kaya yafice zuwa dining inda Amal ke zaune tana jiransa itama idanun nata sun kumbura sunyi ja. Serving nasu abincin tayi kamar yadda suka saba a plate d’aya sukeci. Sede ko kad’an yau Anas baici. “Ya Anas kayi hak’uri dan Allah kaci, karka zauna da yunwa.” cewar Anas. Hawaye taga na cikowa idanunsa, hannu tasa ta tare “Ya Anas kasan baran iya jure kukan kaba please kayi hak’uri.” Be iya yace mata komi ba hannu kawai ya aza kanta tare da mata murmushin dole sannan ya kai spoon d’aya baki bayasan jin Amal na had’asa da Allah kwata kwata spoon biyar yayi yace mata ya k’oshi. Yabari su Abuu su raka TV station d’inma yak’i yana isa wajen ‘yan press tunda ga waje suka soma binsa har sanda ya shiga ciki. Bayan an basa kujera ya zauna suka soka jero masa tambayoyi wanda kad’an daga ciki ya amsa sauran kuwa kuka suka sa sa haka fa kamar d’an yaro Anas ya bud’e dandalin kuka a TV station su kuwa se recording suke direct ana uploading a news *Nigeria’s most youngest billonaire.* Ba’a gama interview d’in bama yatashi yafice dan yadda kuka yafi k’arfin sa. He wanted to be strong amman ina bare iya ba, besan dawani damuwa ze fara handling ba, na Ummimi ne ko kuwa na ‘yar dayayi raping ko na mutuwan Baba kokuwa na managing babban enterprise da Baba ya bar masa. Yakasa tunani giya kawai ne in yasha ze warkar masa da wannan damuwa gidan giyan ya koma ya sake buguwa sannan yafito ya kwanta cikin motarsa har bacci me nauyin gaske ya iske sa. ****** “Ya Fannah yi sauri kizo kiga abin tausayi, hurry!” Afrah ta danna wa Fannah dake kitchen kira. Wanke hannu tayi tafito da wuri. “Kiga yadda d’an Alhj Muh’d ke kuka, Allah sarki.” cewar Afrah. Fannah na kai dubanta kan TV’n taga Anas zaune kan kujera da hanky rik’e a hannayensa biyu ya rufe fuskar sa dashi se kuka yakeyi kamar d’an yaro se kace besan da camera kota ina a gaban sa ba. “Allah sarki!” tace “Allah jik’an Alhj Muh’d, yasa k’arshen wahalarsa kenan.” “Ameen” Afrah dake jin kamar tayi joining Anas suyi kukan tare. “Kinsan kuma me worse part d’in? Fannah ta kad’a kai. Akace a idan Anas d’in Baban nasa ya rasu, yana ji yana gani mutuwa ta musu katanga, Allah sarki!” Tausayi Fannah taji yabata jibi yadda yake kuka sekace bashine mara mutunci me gasa wa mutane magana ba, sekace ba shine me uban jijji dakai ba Allah sarki rashi. Dan yadda Anas ke kuka yasa ta fito daga d’akin ko fuskarsa yakasa bari agani tasan sarai ta k’ara minti d’aya a d’akin kuka zata soma dan hawaye bai bata wuya ga kuma uban tausayi... Haka fa tun daga ranan rayuwar Anas ya lalace yafi na da worse ba aikinsa se shaye shaye barin gida ma gabad’aya yayi ya kama hotel yadda yake shaye shayensa hankalinsa kwance. Safe, rana, yamma, dare Anas na rik’e da bottle na giya a hannu yana sha. Da rasuwan Baba yau sati biyu kenan amman Anas ji yake kamar yau yau d’innan Baba ya rasu sau kusan kullum yake kai ziyara gidan Baba, masu aiki ya nemo dasuna kula da gidan, a rana se anyi shara da mopping sau biyu wane akoi mutum ciki. Tun rasuwar Baba kuwa ya rufe company’n har yau ba’a bud’e ba masu aiki a wajen ba yadda basuyi dashi ba ya bud’e su koma aiki amman yak’i shi a tunaninsa bare iya handling ba bayasan ya b’atawa Baba koda k’wayan zarra ne cikin company’nsa. Allah kad’ai yasan wahalar dayasha kafin yasamu ya gina wannan sky scrapper saboda haka yake jin tsoro sosai kar yayi wani abu yayi ruining abu ciki. Kusan sati uku ake nema yau Anas yak’i bud’e company ga on going projects dayawa nan barkate. Daga k’arshe sanda ‘yan manya manyan wajen suka je suka ma Abuu bayanin komai sannan ya ce musu zema Anas d’in magana. Bayan tafiyar mutanen, Ummie dake taya Amal tsifa tace, “Ya Ibrahim wallahi Anas tausayi yake ban, ba laifinsa bane yaro yake har yanzu dudu shekarunsa 24 nefa, he is still young.” “Saisa yakamata ya bud’e office d’in, yayi hak’uri ya rungumi k’addara k’in bud’e company’nsa ba taimakasa masa zaiba kin deji abinda masu aikin nasa sukace akoi on going projects dayawa kuma koba dan wannan bama yau ace Alhj Muh’d na raye ai bareyi farin ciki da abinda Anas keyi ba. Kowa ya tausaya masa shiima yayi hak’uri ya tausaya wa kansa.” Shiru Ummie tayi ta giad’a kai. Amal kuwa idanta tuni suka cike da hawaye rabuwanta da sa Ya Anas a ido har tamanta tun da yabar gidan kota kirasa wani sa’in ma bai d’ agawa yadda zakusan lallai Anas yashiga wani erin yanayi kenan. Ace Amal ma gabad’aya yak’i picking call nata. Allah sarki! Anas na zaune k’asan carpet a hotel room nasa da giya hannunsa se sha yake ba makawa, gashin kansa ya tarwatse wane na mahaukaci, d’akin duk warin giya yake. Ko ina kwalb’an giya kuke gani ko masu giara sunzoyi bai barinsu su shiga. Kan gadon ne kawai kenan tsatsaf shima d’in saboda ya k’aurace wa kwanciya kai ne a k’asa yake kwanciyarsa yanzu. Wayarsa dake kan gado ya soma ringing haka yana ji amman yakasa koda d’aga k’afa bale yaga kowaye. Haka ya d’aga giyan hannun san yakai baki sanda ya kurb’e tas sannan ya wurgar a k’asa kamar yadda ya saba. Bajewa kawai yayi a k’asan tare da zira wa ceiling ido. Can wayar tasan ta soma ringing again nanma yanaji be d’aga ba se a karo na uku yayi rarrafe ya d’aga idanunsa wani dushe dushe suke gani mai yama kasa gane wake kira kawai picking up yayi ba tare da yace komi ba. “Hello Anas?” Cewar Abuu shirun dayaji yasa yasake fad’in “hello? Anas baka ji ne? Hello?” Ai kawai Anas ya fashe da kuka cin wayar kamar d’an yaro. Hankalin Abuu in yayi dubu be tashi ba gashi basu san wani hotel Anas ya kama ma. “Anas! Anas until when zaka koyi rungumar k’addara ne wai? Kasani Babanka ya riga y rasu duk wannan abinda kakeyi ba dawo dashi zeyi ba. Haba! Mana Anas sekace bana miji ba, man up please. Kap kowa jira yake ka bud’e company’nka amman kak’i se yaushe wai? Iyye?” Shiru kukeji ba response ko kukan ma yadena ji. “Hello? Anas!” Aikam tuni Anas yayi hanging up call d’in se kuka yake ba makawa. Shi har yanzu be yarda cewa Baba ya tafi ya barsa ba, Baba yatafi yabar masa company’nsa daya kula dashi. Yana cikin kukan Shettima ya kira yanaji yak’i d’agawa kusan missed calls biyar sannan ya d’aga nanma shiru yayi bece komi ba. “Hello Ya Anas” muryan Shettima ya jiyo. “Ya Anas kana ina?” Shiru yayi be amsa saba. “Ya Anas dan Allah kana ina? Wallahi duk mun damu ka fad’amin inda kake.” Amsar wayar Amal dake kuka tayi “Ya Anas yanzu seka tafi kabarmu dan Allah ka dawo gida” ta kuma fashewa da kuka. Jin kukan Amal yasa sa magana bayan ya daidaita muryarsa dan kar tagane a bige yake. “Shhh! Kinji Angel bar kuka, zan dawo amman ba yau ba.” “Toh kana ina?” Ta tambaya. “Ina nan cikin Maiduguri.” Amsar wayar Shettima yayi “Ya Anas tell me ina kake inzo in sameka.” “Nooo bareyi kazo ba right now am drunk banasan su Abuu da Ummie suzo...” Aiko ya fara magana kamar zararre “kar su zo sugan ni ahaka sukamu da cancer” bama ciwon zuciya ba. Yad’anyi dariya “wayasani ko suma su mutu.” “Ya Salam!!!” Shettima ya fad’i. “Me ya same sa Ya Shettima?” Amal ta tambaya tana kuka. “Ba komai” Shettima ya mata k’arya “jeki ina zuwa.” A sanyaye ta tashi ta fice. Tana fita Shettima ya dawo kan wayar. “Ya Anas what are you saying? Yanzu fisabilillahi tun tafiyar ka can kata shaye shaye? Ina kake yanzu.” “Chill little bro! Karka damu am somewhere safe.” “Ya Anas ka fad’amin inda kake inzo in duba ka please kaji?” “Saboda kazo dasu Ummie da Abuu sugane ina shaye shaye?” Anas yafad’i idanunsa suna kakkafewa besan sanda yabada address d’inbama kawai ya zarce bacci. A gurguje Shettima ya fito ya samu su Abuu a parlour duk hankalinsu ya tashi. “Ya haka? Ina zuwa?” Abuu ya tambayi Shettima. “Wajen Ya Anas zani Abuu.” yabasa amsa. “Tsaya muje tare toh mana.” “A’a Abuu please kayi hak’uri yace inje ni kad’ai bareji dad’i ba in ya ganmu duka kubar damuwa Ya Anas is somehwere safe.” “Anya kuwa Shettima?” Cewar Ummie cike da damuwa. “Kabari muje duka mu gansa dan Allah.” “Ummie please kar mu fara ce in ce, Ya Anas made it clear to me ni kad’ai yakeson in je kuyi hak’uri.” “Bakomai Shettima Allah kare kakuma isar masa d sak’on.” Abuu ya fad’i. “Toh Abuu” nan ya ja mota ya fice. Daidai ya isa harabar hotel d’in yafito bema san room number’n da Anas ke ciki ba, ko daya tambayi Anas d’in kuwa shima ce masa yayi besani ba tsantsan yadda ya bugu kawai. Reception ya wuce yayi tambaya k’in fad’i masa tayi acewarta ko yazo cutar dashi ne. “‘kaninsa ne ni can’t you tell? Bakiga muna kama bane?” ya daka mata tsawa. “Now tell me his room number.” Kallon fuskarsa tayi a tsorace sannan taga eh fa suna kama “I'm sorry sir room 21 CEO’n Flames Enterprises yake.” Da gudu ya haura sama zuwa room 21. A bud’e ma ya tarar da k’ofar yana sa kai warin giya ya masa sallama. Salati kawai yake yana bin d’akin da kallo kwalb’an giya sekace na siyarwa. Toshe hancinsa yayi tare da rufo k’ofar akan gado ya tsinci Anas yayi ruf da ciki se bacci yake. Kwata kwata singlet ne a jikinsa seda short nicker. Gashin kansa daya tarwatse ya rufe kad’an daga cikin fuskarsa. Juyar dashi Shettima yayi tare da kiran sunan sa. Shiru kukeji ba amsa. “Ya Anas! Kana jina?” “Uhmmmm” ya fad’i idansa rufe yana bacci. Giara masa kwanciya Shettima yayi tare da rufe sa da bargo sannan yakoma k’asa yakira masu aiki suka kimtsa d’akin tsaf aka sa room freshner me uban k’arfi da dad’i dan kora warin giyan. Baccin awa uku Anas yayi sannan ya farka a hankali ya soma bud’e ido ya saukesu kan Shettima. K’ok’arin zama yake Shettima ya taimaka masa. “Ya Anas how are you feeling?” “Yaushe ka shigo nan? Ya kasan ina nan?” Tambayar da ya masa kenan. “Kai kafad’a min, but it doesn’t matter. Ya Anas this has to stop. Ya isa fisabilillahi me damuwarka ne? kai bakasan meh k’addara bane a rayuwa? Kashe kanka kakeson yi kwalaban giya kusan 30 a d’akinka hauka ne kuma abin?” Ba tare da ya amsa saba yace, “inasu Abuu kataho dasu ne?” “Ban taho dasu ba amman believe me ina komawa gida zan sanar dashi da Ummie wannan halin naka na shaye shaye tunda you are not ready to change. Ina ka tab’a jin dan an ma mutum rasuwa seya soma shaye shaye haka? Haba mana Ya Anas.” “I’m sorry” ya fad’a a hankali cike da jin haushin abinda yayi. “Shettima I’m sorry, giyan ne kawai in nasha nakejin problems d’ina sun tafi. Shettima kubar ganin laifi na please abubuwa ne sun min yawa I'm just 24 baran iya managing babban Enterprise kamar na Baba ba. Baran iya ba, it is beyond my will.” Sekuma ya fashe da kuka. Da had’in Allah da Annabi da kuka sannan Shettima yasamu yayi convincimg Anas kan bud’e company’n. Wanka yasa sa yayi yana fitowa ya masa ordering abinci sosai Anas yasamu yaci. “Thank you Shettima, bansan ya zanyi ba without you.” Hugging nasa Shettima yayi “me too brother dan Allah ka rage shaye shayen nan kar alcoholic level naka ya haura yazama toxic, dan Allah.” Hugging nasa back Anas yayi “in shaa Allah zan rage.” Bayan sun sako juna Shettima yace, “lets go ga kayakin ka nan duk na shirya maka.” Tare suka sauk’o bayan Anas ya biya bills nasa suka dawo gida cikin motocin su. Amal na zaune bakin k’ofa tun d’azu tana jiran dawowarsu gate taji an bud’e da sauri takai dubanta ganin motan Ya Shettima k’aramar benz C230 yasa ta koma baya ta zauna tana sake juyawa kawai taga motar Ya Anas tsalle ta daka tayi wajen parking da gudu yana fitowa sukayi huggibg junansu sosai. “I miss you Ya Anas” tace tana hawaye. *© miemiebee* *Yabo a gareku ya zama dole ‘yan duniyar littafafan hausa’n Baby zahrah. Allah bar k’auna I love you lodi lodi.* beeenovels.mywapblog.com [12:47, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 1⃣8⃣ “I miss you too my Angel, bar kuka barin sake tafiya ba, I’m back forever.” “Yeyy!” tasake hugging nasa. Bayan sun shigo su Abuu da Ummie duk sukayi hugging nasa sun mugun jin dad’in dawowansa. “Sannu da zuwa Baba” na cewar Ummie, “kar ka sake tafiya dan Allah.” “In shaa Allah Ummie.” Anas yayi assuring nata. “Erm Anas I’m sure Shettima ya sanar dakai halin da ake ciki koh? Ma’aikatan company’nka har gidan nan sukazo suna rok’o na in maka magana sukoma office.” “In shaa Allah monday zan bud’e Shettima ya fad’a min komai. I’m sorry baran sake barin gidah ba. Problems ne suka min yawa Abuu bansan ta ina zan fara solving ba.” “Anas just know we are here for you running is never a solution.” “In shaa Allah Abuu barin shiga daga ciki.” Amal dake mak’ale kan cinyarsa ta tashi tare da k’ara mak’ale hannunta a nasa. “Kekuma Amal ina zaki?” cewar Ummie. “Zanbi Ya Anas d’akinsa.” “A’a kinga Ya Anas ya gaji yana neman hutu da bakin kinnan zaki damesa.” “Ummie mana, barinyi surutu ba” tafad’a tana bubbuga k’afa. “Don’t worry Ummie, taho muje my Angel.” Gwalo Amal tama Ummie sannan tabi Anas d’akinsa. Bayan ya rage kayan jikinsa ya haura gado tana zaune kan couch “Ya Anas ina kaje daka tafi?” Ta tambayesa. “Hotel Angel.” “Ohhh! kasan kowa yayi kuka daka tafi, tunba ni ba we all miss you blue eyes.” Ido ya zaro “Amal ina kika san sunan nan?” K’arya tayi “babu kawai ni na had’a.” “Yau ni kike ma k’arya? Saboda kinsan password d’ina kika fara min shisshigi a waya ko?” ya tambayeta. “A’a fah Ya Anas ranan ne wata ta turo message lokacin ina game a wayan shine... Shine..” Sekuma tayi shiru. “Shine kika bud’e kika karanta koh?” “I’m sorry Ya Anas please karka canza password d’in.” “Toh naji barin d’an kwanta koh?” “Okah ba-bye” nan ta mik’e ta fice. _Washegari..._ Yau ta kasance Monday da safe Anas ya tashi ya shirya cikin black suit, black shirt da white necktie wanda yamun masa kyau bayan yayi breakfast yaja benz na sa ya fice zuwa office. Daidai k’arfe takwas ya isa mutane turum ya tarar bakin k’ofar duk shi suke jira yana fitowa sukayi kansa suna gaishesa da “Boss” bayan ya bud’e office d’in ya shiga elevator zuwa last floor inda new office nasa yake. Kallon office d’in kawai yake se gani yake kamar Baba ze shigo ya zauna kan office. Ba abin arzikin dayayi ranan inbanda tunanin daya tayi seda signing papers da ake ta kawo masa. Sosai su Kacallah da Yunus suka yi condoling nasa kamar yadda duk sauran ma’aikatan suka masa. Sam be saba ba in suna kiransa da Boss. Aranan akayi renovating office d’in yakoma komai na ANAS IBRAHIM FAUZY. Office ne babban gaske me ciki biyu wanda harda d’aki ciki. Fridge, California bed, TV ba abinda babu ciki. Da yamma da misalin k’arfe 4:00PM daidai lokacin da suka tashi bayan Anas ya tattara stuffs nasa Kacallah ya shigo. “Uh sorry Boss bansan har ka tashi ba, wallahi seda aka tashi Ahmaz investment daga Kaduna suka kawo wannan kuma gobe zasu koma. “I’m so sorry please.” “Bakomai” Anas ya fad’i yana murmushi “kawo inyi signing.” “Thank you Sir! You’re so kind.” Nan Anas ya zauna bayan yayi signing Kacallah ya sake masa godiya yakai da bakin k’ofa Anas yace, “uhm Kacallah are you free?” “Yes Sir wani abu ne?” “Ba abinda zanyi yau nace ko zakazo mud’an fita maybe muje muyi having snack tare I need someone to talk to.” “Oh yes ofcourse Sir barin kai wannan kafin su tafi.” Kai Anas ya giad’a masa “thank you” “The pleasure is mine sir.” Nan yafice bada dad’ewa ba ya dawo suka shiga elevator tare. A motan Anas suka fice, “so ina kakeso muje?” Anas ya tambayesa. “Duk inda kace will be fine Sir.” Cewar Kacallah cike da girmamawa. D’an murmushi Anas yayi “in mu bibbiyu ne kana cemun Anas kawai.” “I’m sorry sir amman baran iya ba, girman ka yayi yawa ace na kiraka da sunan ka. I’m sorry please.” “Tun da haka kace fine, so ina zamuje.” “Muje Fahmaz coffee shop Sir.” “Fahmaz Fahmaz...” Anas ya tsaya nazarin abu “ohh sune wanda in an kirasu waitresses nasu basua magana a wayan nan koh?” “Ahha Sir nakega basu gane ko kai waye bane. Muje chan d’in please you’ll like their services.” Ba musu Anas ya tuk’asu zuwa coffe shop nasu Fannah. Bayan yayi parking suka fito suka shiga tundaga bakin k’ofa aka fara tarerayar su Anas anga Nigeria’s most youngest billonaire. A special table suka zauna. Ya suleiman ne yazo ya musu sannu dazuwa da kansa sannan ya d’auki order’n su. “Mr. Fauzy is my honour having you here at my coffee shop what can I get you?” Ya fad’i yana washe 32. Kai Anas ya giad’a masa sannan ya dawo da kallon sa kan Kacallah. “Me zamuyi ordering?” “Sir nikuma zan mana ordering please do, ni ai duk abinda ka mana ordering I’m fine with it.” “No Kacallah I insist ka mana ordering. Feel free with me please.” “Tunda kace haka sir OK. Akawo mana caf`e lat`e.” “Unfortunately bana shan coffee.” Anas ya fad’a yana kad‘a kai. “Ohh sorry sir but da ka gwada gaskia nan coffee shop suna k’ok’arin yin coffee.” “Yes Sir” cewar Ya suleiman “ka gwada coffee’n mu I’m sure you will not regret it, please.” “Tunda kunyi insisting okay. Get us two caf`e lat`e.” “Thank you sir” sannan ya fice yana shiga ciki ya soma k’olla wa Fannah kira. Nan tafito tana daidaita hijabinta. “Yes Boss!” Ta fad’i cike da gatsine. “Yawwa yau zo ke zaki had’a coffee’n nan. Inason ki had’a coffee’n da baki tab’a had’awa ba.” “Tohhh d’an shugaban k’asa ne yazo coffee shop namun?” Ta tanbaya tare da d’age gira. “You will find out in kika kai musu. Two cups, ki had’a yayi kyau please Fannah give it your best. Table 03.” “Okay Sir” tace tana dariya. Nan ta hau had’awa bayan 3 minutes ta gama ta aza kan tray sannan ta fice. Kanta a k’asa tana kaiwa zuwa table 03 ta gaishesu tare da ajiye wa a gabansu. “Thank you” Kacallah ya fad’i nan ne ta d’aga kai ta kallesa “you’re welcome” ta masa murmushi jin d’ayan bece komi ba yasa ta juya ta kallesa lokacin kuwa hanky Anas ya cire yana goge fuskarsa se bata samu ta gansa ba. Tana ajiyewa ta fice. Anas na kai coffee’n baki yaji k’amshi sosai. Dayasha kuwa yaji dad’insa sosai tunda yasan kansa be tab’a shan coffee me dad’i ba kamar na yau ba last time dayasha a London kwata kwata be masa dad’i ba sesa yabar sha ma. Be cire cup d’in daga bakinsa ba sanda ya kurb’e duka. “Wow! coffee’n nan yayi dad'i sosai, this is the first time coffee yamin dad’i. In ba damuwa inason in k’ara.” Murmushi sosai Kacallah yayi “I told you sir. Waiter!” Ya kira wani na miji me uniform “caf`e lat`e zaka k’aro wa Boss d’ina.” “Okay” ya fice nan da nan yaje ya had’o ya kawo saidai da Anas ya tab’a ya ji na d’azun yafi dad’i. Da kyar ya had’e dan yadda ya yamutsa fuska yasa Kacallah tambayan ko lafiya. “Sir are you okay?” Ajiye cup d’in yayi “ba wannan nasha d’azu ba. Irin na d’azu nakeso.” Anas yace. “Sir” cewar waiter’n. “Caf`e lat`’n daka buk’atan nefa kalan na d’azu.” Tsawa Anas ya daka masa “No!” “nace ba eri d’aya bane kaje ka sake had’o min irin na d’azu.” “But sir-” “I said now.” Anas ya sake daka masa tsawa. A tsorace yabar wajen. “Sir I'm so sorry please” cewar Kacallah. “Is okay ba komai.” Anas ya tabbatar masa. Shigar waiter'n ciki yasamu Ya Suleiman. “Ya akayi Harauna?” Cewar Ya Suleiman. “Ya Suleiman CEO’n Flames Enterprises ne yace na had’o masa caf`e lat`e na had’o masa kuma wai ba irinshi yakeso ba, wai ba irinsa yasha d’azu ba.” “Omg!” Ya Suleiman yayi exclaiming. “Ina Fannah? Jeka kirata ita ta had’a masa kace tazo ta barinje in basa hak’uri” da “toh” suka rabu. Isan Ya Suleiman cikin shop d’in yayi kan table nasu Anas. “Sir please kayi hak’uri anje kiran yarinyan data had’a na farkon ne yanzu zata zo kayi hak’uri dan Allah.” “Make it quick inada abinyi please.” Cewar Anas nan Haruna yafito “Ya Suleiman Fannah bata nan ta tafi yanzu Asma’u ke fad’a min.” “What!?” Cewar Ya Suleiman. “Taya zata tafi? This is the first time take barin nan bata fad’a min ba.” Nan ya kewayo da kallonsa kan Anas. “Mr. Fauzy I’m so sorry please yarinyar data had’an ta tafi gida nakega emergency ne yataso but akoi wata itama ta iya had’awa sosai barin mata magana.” Ran Anas tafasa yake, “then make it quick!” Yafad’a a tsawace. Bayan ‘yan mintuna Asma’u tafito da coffee’n Anas. Tana ajiyewa ya d’auka yayi sipping nan ma taste d’in be masa ba wurgi ma yayi da cup din coffee’n ya zube a yayinda cup d’in ya tarwatse b’ari Asma’u ta soma. “Wai ace nan cofee shop amman ba me iya had’a coffee?” Ya Suleiman ne yafito yana ganin irin b’arnan da Anas yayi shi bama wancan ba kar Anas yasa ayi sueing coffee shop nasu. Hak’uri ya soma basa. “Mr. Fauzi wallahi wanda ta iya had’awan ne ta tafi gida.” “Wacece ita?” Anas ya tambaya rai b’ace. “Fannah ce Sir Fannah Aleeyu.” “Koma wace ita call her now kace mata ta dawo and make me coffee.” “Yyesss sir” Ya Suleiman ya amsa baki na rawa. Wayarsa ya ciro ya kira Fannah har ta tsinke bata d’aga ba se a karo na biyu. “Hello Fannah ina kikaje? Ki dawo please is urgent.” “Ya Suleiman jikin Baba ne yatashi yanzu haka asibiti zamu kaisa bareyi in dawo ba.” “Fannah dan Allah su Mama barasu iya kaisa ba? Nasan lafiyan Babanki means alot amman you are needed here rashin zuwanki ze iya jefa lafiyar coffee shop in mu cikin matsala please.” “Ya Suleiman if only I can come, baran iya barin Baba ba dan Allah kayi hak’uri I have to go” karap ta kaste wayar. Fuskar Ya Suleiman kad’ai amsa ce ga tambayar Anas. “So?” Ya tambaya “Sir we are so sorry amman yarinyar barata samu zuwa ba.” Kallonsa Anas yake “kasan ko ni waye ne? Nace ka kira Fannah take ko meh and tell her tazo ta had’a min coffee.” “Mr Fauzi mahaifinta ne ba lafiya saisa barata iya zuwa ba.” Anas najin ance mahaifinta yaji ya hak’ura. “Okay” yace tare da ajiye musu N1,000 kan table d'in yaja jakarsa a yayinda Kacallah yabi bayansa. Mamaki ne yacika Ya Suleiman da Asma’u daga jin ance mahaifinta kawai ya canza mind nasa ga kuma dubu d’aya daya ajiye musu ba tare da ya amshi chanji ba. Shide gode wa Allah yayi. _Wahsegari..._ Da misalin k’arfe uku da rabi Anas ya zo coffee shop nasu Fannah shi kad’ansa. Tun jiya ya kasa bacci dan kwad'ayin coffee’n dayake tayi. Sam yarasa meke masa dad’i duk abinda yasa a bakin sa bai masa dad’i shi coffee d’in kawai yakeso duk ya k’osa yasake sha. Bayan yashigo aka karb’esa da girmamawan daya cancanta, nan yayi ordering caf` lat`e. Bayan yaron ya juya Anas ya kirasa “and kace Fannah... Fannah Aleeyu ce ta had’a and no one else okay?” “Okay” yaron yace masa. Yana shiga yasamu Fannah zaune tana buga gamw a wayarta yakai mata order’n ba tare da ta kallesa ba tace, “wai nikad’ai kake gani anan ne Boy? Ga Asma’u da Allah ka kai mata kaga game nake yi hak’uri.” “Ya Fannah shi wanda yabada order’n ne yace ke zaki had’a.” Baki wangalau Fannah ta bud’e lallai ma “yaushe aka fara wannan sabon salo? Coffee ba coffee bane waikam. Koma waye ne yayi hak’uri barin had’a ba tunda ba shift d’ina bane, Asma’u da shift nata ne ta had’a.” Daidai lokacin Asma’u ke shigowa cikin kitchen nasun. “Yawwa gara ma da kika shigo. Gashi caf`e lat`e zaki had’ama wani kiyi sauri.” “Waye ne?” Asma’u ta tambayi yaron. “Nima bansan sunansa ba.” “Ya yake? Fari ne yanada blue eyes?” “Eh” yaron ya giad’a kai. “Fannah dan Allah kiyi hak’uri ki had’a masa wallahi shine wanda yazo jiyan.” “Wai waye shi duk kika bi kika tsure haka?” “Fannah wallahi shine, Mr Fauzi d’an marigayi Alhj. Muh’d.” “shi???” Fannah tafad’i tare da zaro ido. “Fannah dan Allah wallahi naki kawai yakeso, jiya nida Haruna muka had’a masa coffee wulli yayi dashi, please Fannah” ta k’are maganar kamar zatayi kuka. “Chabdi!” Cewar Fannah “ai gara ke ni da kike gani nannan wallahi banasan abinda ze sake had’ani da Anas d’innan ranan har kuka sanda yasani.” Daidai lokacin Ya Suleiman yashigo ransa b’ace “wai Fannah meke damunki ne? Bakisan da abinda kikeyi zaki haddisa mana problem ba? Wuce ki had’a masa coffeen kinsan ko waye shi?” “Ya Suleiman amman shift na Asma’u ne fah.” Katse ta yayi “amman kuma ke Mr Fauzi yakeson ki had'a masa off you go.” Zata k’ara magana ya daka mata tsawa “now!” hawaye taji na ciko mata a sanyaye ta mik’e ta had’a masa takawo gaban Ya Suleiman ta ajiye. “Gashi.” “Aww nikuma zan kai masa? Kikai masa yana san miki magana.” “Ya Suleiman dan Allah kayi hak’uri kaba wata ta kai masa wallahi banasan magana dashi dan Allah.” “Fannah I can’t say no to him kawai kije ki rufa wa coffe shop namu asiri.” Zata sake magana ya fice juyowa tayi ta kalli Asma’u da take ta kau da kallonta elsewhere. Miyau ta had’iye sannan ta fice kaiwa Anas kujerun ta duba sannan can ta hangesa dukda bata ga fuskarsa ba amman daga farinsa ta ganesa. A hankali ta k’arisa kan table d’in ta ajiye a lokacin yana kan waya yana kallon window. Tana ajiyewa ta juya zata tafi holding wayar yayi “Boss naki be fad’a miki inasan miki magana bane?” Ya fad’i authoritatively ba tare da ya kalleta ba. Cak ta tsaya tare da kewayo wa... *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:47, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 1⃣9⃣ Wayar da yakeyi ya cigaba da, tafi minti uku tsaye sannan yayi hanging, ba tare da ya kalleta ba ya d’au coffee’n ya kai baki be cire ba sanda ya kwankwad’e tas mamaki ne ya cika Fannah datayi mutuwan tsaye tana kallonsa cike da mamaki waiko d’umi d’umin coffeen ma baiji? “I will appreciate it in zaki bar kallo na haka kinemi waje ki zauna.” cewar Anas. Miyau ta had’iye wai shi ya yake gane mutum na kallonsa ne? A kunyace taja kujera ta zauna d’an nesa dashi har yanzu be d’ago kai sunsa juna a ido ba. Bayan ta zauna ya d’ago kyakkyawan fuskansa ya aza blue eyes nasa kan Fannah. Idanunsu na had’uwa Fannah ta saki salati. “Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!” tare da dafe k’irjinta. Kallonta Anas yake cike da mamaki. Kallon cikin ido suke ma juna shide baya manta fuska yau ya soma sa Fannah cikin ido mesa take kallonsa kamar ta sansa? “Hey!” Ya fad’i da kallon ya ishesa. “Are you okay?” Shiru har yanzu tayi tana kallonsa tana tuna ina ta tab’a kallonsa, wannan idanu tasan ta tab’a sata cikin idanunta amman takasa tuna a ina. Tayi tayi amman takasa. Table d’in ya buga firgit ta kyafta idanunta tadawo reality. “Aljani kika gani neh?” Ya tambayeta. Kai ta kad’a masa. “Better” ya fad'i relieved. “So kece kike had’a wannan coffee?” Shiru tayi bata amsa ba se kallonsa take wanda har yafara feeling uncomfortable. “Please na kiraki nanne to give you an offer bawai ki tsaya kina kallo na ba, hold it after natafi you can admire me.” Kut lalle ma wannan Anas, jijji dakai ya maka yawa, well kanada kyau amman ni ba kyanka nake kallo ba cewar Fannah a zuci. “Ba kallonka nake ba” ta fad’a tare da kawar da kanta daga ganinsa. “Allah sa you mean what you said just now. So ke kike making coffeen nan?” Kai ta giad’a. “See Fannah kike koh?” Nanma kai ta giad’a. “Damn it!” Ya buga table d’in a tsorace ta d’ago kai tana kallonsa. “I hate it in ina wa mutum magana yana using body signal, kimin magana as I do you, clear?” B’ari take ta giad’a kai take tace “eh.” “Good” yace sannan ya cigaba “maganan gaskia I like your coffee.” “Thank you”+ tace a hankali. “And inason ina sha kullum like safe rana yamma dare all the time.” “Sir but coffee shop namu k’arfe shida muke rufewa kuma ni 2:00PM -3:30PM ship d’ina yake k’arewa.” Tafad’i tana kallonsa “Exactly! sesa na taho miki da offer yau. And for the last time kidena kallo na will you?” Kau da kanta tayi da alqawarin barata sake kallonsa ba so take ta tuna ina ta tab’a ganinsa sarai tasa wannan blue eyes nasan sede ta rasa a ina ta tab’a ganinsu. “So kinsan ni waye ne ba sena fad’a miki ba Anas Ibrahim Fauzi CEO’n Flames Enterprises inason inyi offering naki better job a company na kina making min coffee 24/7 meaning duk lokacin da nakeson shan coffee I’ll give you a call and komin me kikeyi a lokacin zaki bari kizo ki had’a min abinda kawai zaki na min kenan and zanna biyanki ko wani k’arshen wata da salary me kyau. So what do you say?” “Mr. Fauzi nagode da wannan dama but am sorry baran iya karb’a ba saboda as you can see ina da aiki a nan kuma am satisfied with it. In zakayi excusing d’ina zankoma aiki.” Tana k’ok’arin mik’ewa ya daka mata tsawa “sit! This should be the last time, ba’a dismissing d’ina sede inyi dismissing mutum clear?” “I’m sorry” tace “now sit.” Ba gardama takoma ta zauna ita bata ga mesa zesa tama wannan arrogant mutumin aiki ba, ita tausayawa masu aiki k’ark’ashinsa ma take. Mutum kullum cikin tsawa da masifa ba dariya? Chabdi! “Nawa ake biyanki anan? I mean whats your salary?” Tambayarsa ne ya dawo da ita daga duniyar nazarin data fad’a. “Mr. Fauzi me zakayi da albashi na, naga kamar its personal.” “Zaki fad’a min salary’n kine kokuma sena sa an rufe coffee shop nakun?” Zaro ido tayi wai wannan wani irin mutum ne? “N10,000 (dubu goma) ne.” D’an murmushi yayi baki rufe wanda kawai dimple nasa ne kad’ai ya lotsa. “N10,000 kad’ai salary’nki? Work for me I’ll pay you double.” Zaro ido tayi. “Ko ya kasa? N30,000 then.” K’ara ciro ido tayi waje “N40,000 toh.” Kai ta sosa “induk yakasa miki toh N100,000 inshima ya kasa tell me ko nawa kikeso I’ll pay you as long as zakina making min coffee.” Mamaki ne yacika Fannah lallai wannan Anas baida matsala jibi yadda yake irga kud’i sekace dutse? “So, you accept my offer?” “Mr. Fauzi kayi hak’uri inasan aiki na anan dukda albashin bame yawa bane amman Allah nasa min albarka kuma i’m satiafied.” “Oh common Fannah karki yaudari kanki dubu goma bare rik’e ki har na wata ba, dubu goman da ake kashewa in just a minute? accept my job ko nawa kikeso I’ll pay you.” “Mr. Fauzi I’m sorry please, nagode zan tafi.” “Kiyi tunani Fannah anytime kika canza mind naki you can call me” hannu yasa yaciro card nasa tare da ajiye mata kan table d’in. “Koda zaki kira karki kira around k’arfe 5:00PM to 8:00PM.” Be jira me zatace ba ya d’au jakarsa ya fice. Hararan card nasan tayi, ta ja tsaki sannan ta d’aga ta karanta, phone numbers nasa biyu tagani kai. “Aiko nasha giyan wake barin kira ka ba, bana buk’atan dubu d’ari d’arin ka mschww” d’aga katin tayi da nufin yagawa karap Asma’u tasa hannu ta wabce. “Ke bani!” cewar Fannah. “Nak’i barin bayar ba. Ke yanzu Fannah Mr. Fauzi gabad’aya yabaki card nasa shine kike k’ok’arin yagawa? Meya sa yabaki?” “Oho! kiya tambayesa ni bakisan wani abu ba tsoro yake bani wannan da blue eyes nasa kuma kinsan wani abu? ji nake kamar na tab’a ganin sa awani waje kuma kamar yadda muka had’u bawai irin yamin mutunci bane kamar... Sharri” Tayi shiru tana kad’a kai “ya Allah a ina nasan wannan bawan naka?” Ta tambayi kanta. “Kefa Fannah anyi mutum yanzu Mr Fauzin ne harzaki wani tambayi a ina kika sansa ko kika tab’a ganinsa? Abinda har office nasa kin tab’a zuwa aikunsha had’uwa.” “A’a Asma’u duk had’uwar mu dashi bamu taba had’a ido dashi ba se yau kuma ayau d’in naji na tab’a had’uwa dashi wani wajen amman nakasa tunawa.” “Kide tuna” cewar Asma’u. “Seki tashi lokacin tafiyar ki yayi.” A sanyaye Fannah ta mik’e, Asma’u tabi bayanta. “Ina jakarki Fannah?” Akoi wayata ciki in cire. “Yana chan kan counter a kitchen please kifito min dashi” murmushi Asma’u tayi sannan tafice zuwa kitchen chan ta d’au jakar Fannah ta bud’e daman bawani wayarta ciki, card na Anas tasa cikin jakar cikin wata zip sannan ta rufe takai wa Fannah. Isar Fannah gida keda wuya ta tarar da Afrah kad’ai a gida har su Mami sunkai Baba kenan ta fadi a zuciya. “Sannu da zuwa Ya Fannah ya haka kuma yau? Tun shigowarki kinyi shiru.” Bayan ta zauna kusa da Afrah tace, “wallahi Afrah wani abu ke damu na.” “Wani abu kenan Ya Fannah?” “Yau Mr Fauzi yazo coffee shop namu-” Katse ta Afrah tayi “dan Allah!? Omg! Kunsamu kunyi magana? Wayyo Allah!” Marinta Fannah tayi a hannu “da Allah kimin shiru. Kinaji ba?” Afrah ta giad’a kai Fannah ta cigaba; “I mean jiya ma yaje shagon namu to da yasha coffee na seyace wai yamasa dad’i yau ma yadawo na k’ara had’a masa.” Afrah zatayi magana Fannah ta katse ta “please kiyi shiru kiji ni.” “Ina kaiki, bayan na kai masa...” Nan ta kwashe labarin komi tabawa Afrah sosai Afrah tasha mamakin erin sokancin da Fannah tayi. A yadda suke shan bak’ar talaucin nan ne har za’a bata aikin dubu d’ari tace battaso? Lallai kam. “Afrah kinyi shiru.” Cewar Fannah “Saboda kin ban mamaki ya Fannah at thesame time kuma kin ban haushi yanzu har a baki aikin dubbai kice bakiso? Seyau nasan bakisan Baba yasamu lafiya gaskia.” “Afrah wace erin magana kike haka? Baki tsaya kinji dalilin dayasa nak’i aikinsan ba fah.” “Toh ina jinki wani dalili ne haka?” Hannunta Fannah ta rik’o. “Wallahi Anas baida mutunci kinfi kowa sanin yadda nake tsoron masifa da tsawa banasan amin masifa shiko Anas ba aikinsa se ma mutum masifa wallahi ko yau danne zuciyata nayi banyi kuka ba daya daka min tsawa. Bayan haka kuma kinga ai bareyi inbar aiki haka kawai da su Ya Suleiman ba, bareji dad’i ba mun saba najima ina aiki dasu kawai dan an bani aiki me kyau se na mance dasu? Na kyauta kenan?” “Haba Ya Fannah mesa masu aiki suke barin gun aikinsu in sun samu me kyau? shi kansa Ya Suleiman inhar yana sanki murna ze miki dan wannan promotion. Dan Allah Ya Fannah ki karb’i wannan aiki, for once a rayuwarmu muma muji dad’in da akeji, Baba yasamu lafiya.” Kad’a kai Fannah tayi “Afrah niba wannan bama. Afrah inada wrong idea da feeling akan Mr. Fauzi yau na soma sasa a idanu na amman kuma ji nake kamar natab’a ganinsa wani waje kuma kamar had’uwan mu sharri ne, Afrah bansan meke damuna ba.” “Lallai! Ya Fannah ai dama kin sha kallonsa mana, ko kin manta shi kikaje office nasa ranan?” “A’a Afrah believe me wallahi duk had‘uwar mu dashi bamu tab’a had’a ido hud’u dashi ba.” “Toh in banda abinki ranan ai na nuna miki shi a TV.” Shiru Fannah tayi tana nazarin abu.. “Kuma fa haka ranan kin nuna min shi a TV lokacin da Babansa ya rasu” zata k’ara magana sekuma tayi shiru “amman fa kaman bangansa ba ma ranan na tuna bangansa ba” “A’a Ya Fannah kituna dakyau kin gansa koda kad’an ne, kinsan dama wani sa’in ai haka ne sekaga kamar baka ga mutum ba amman ka gansa next in kuka had’u kuma seka ta wondering ina kuka tab’a had’uwa. In bahaka ba ina ke ina had’uwa da Anas d’an billonaire ko kin manta a ture can London yayi rayuwarsa. Bansani ba ko kema kinje London d’in a mafarki” Afrah ta fad’a taja dariya. Maketa Fannah tayi “LOL kuma fa kinyi gaskia nakega hakan ne a TV na gansa ranan in bahaka ba kam ina zan had’u da mutum kan Anas.” “Yawwa ‘yar garin so yanzu zaki karb’i aikin?” “Eh” tama Afrah k’arya dan kar taji haushinta amman kam har cikin ranta bata san amsar aikin, kuma bataga abinda ze sa ta amsa ba. Gara ta soma neman sabon aiki datayi aiki k’arkashin Anas, mutum ne kullum cikin masifa baya murmushi bale dariya. Sekace dodo! Da daddare da misalin k’arfe tara bayan su Fannah sun idda sallah suna shirin kwanciya wayarta ya soma ringing tana kai dubanta taga Ya Suleiman cike da mamaki ta d’aga dan kuwa be tab’a kirarta warhaka ba se addu’a take Allah sa ba magana ze mata gameda Anas ba. “Assalamu Alaikum Ya Suleiman.” “Ff... Fannah!” Se jin muryar tasa tayi na rawa. “Ya Suleiman meya faru? Wani abu ne? Ya muryarka ke rawa?” “Fannah shagon mu... Shagon mu Fannah!!” “Ya Suleiman dan Allah meya sami shagon namu please tell me” hankalinta tashe take maganar. Afrah dake gefenta itama ji tayi zuciyarta na bugawa. “Shagon mu yakama da wuta Fannah k’urumus ya k’one ba abinda aka samu aka cire. Wutan NEPA ne yasoma gobarar kafin akira fire service k’urumus komi ya k’one.” Salati Fannah keyi ba makawa. “Innalillahi!” take idanunta suka cike da hawaye “Ya Suleiman kayi hak’uri mud’au wannan a matsayin jarabawa dole kayi hak’uri ka rungumi k’addara innalillahi! Gobe in shaa Allahu zan fito dare yayi yanzu dana fito am so sorry kayi hak’uri dan Allah.” “Nagode Fannah” ahaka sukayi sallama. “Ya Fannah meya faru?” Cewar Afrah. “Afrah shagonmu ya k'one wutan NEPA ne yasoma gobarar.” Salati Afrah tayi sannan tayi calming Fannah dake hawaye down. “Daman kinada niyyan barin aikin segashi dalili kwararre ya zo ayyah, Ya Fannah da rabon Allah baisan kiyi witnessing a day without a job.” Kallonata kawai Fannah take cike da damuwa ita shikenan nata ya k’are mesa hakan ze faru da shagonsu? Yanzu ya zatayi da kud’in asibitin Baba? Dole a gobe taje tasoma neman aiki.” Washegari da sassafe ta tashi taje ta shagonsu k’urumus komai ya k’one abin tausayi. Ya Suleiman da Babansa da angansu anga wanda suka kwana suna kuka. Condoling nasu tayi gashi dama k’arshen wata yayi jiran albashi take ta k’arisa biyan kud’in asibitin Baba gashi yanzu da abinda yafaru ba su ba albashi dan koda za’a bata ma barata amsa ba da wannan masifar daya same su. _One week later..._ Yau k’imanin sati kenan Fannah na neman aiki ba rana ba dare amman har yau ba labarin aiki, abin har kuka yake sata ga kud’in asibitin Baba ‘yan asibitin sun dameta harda cewa in bata k’arisa biya ba zasu kaita gun ‘yan sanda. Abinci ma yasoma k’arewa masu agida abinde ba kyau. Ita nadaman mesa ta yasar da card na Anas ma take ta hak’ura da duk walak’anci da masifan da ze mata inhar ze bata kud’i tabiya kud’in asibitin Babanta. Kuka tasha a waje sannan tashigo ciki. Mami da Baba da Aiman suna d’akinsu. Tana k’arisawa d’akinsu da Afrah ta tare ta zaune kan gado yau ko chatting d’inma battayi dan ba kud’in kati. “Afrah ba magana ne?” “Ya Fannah me zance miki? Nariga na gaya miki abinda yakamata. Kinada halin da zaki warkar damu daga wannan hali amman kika k’i. Kalli yadda kowa yake shan wahala haba Ya Fannah dan Allah.” “Afrah wallahi ba haka bane na miki k’arya dana ce miki zan karb’i aikin da Mr. Fauzi yabani wallahi tun a ranan daya bani card nasan na yasar bansan ya zanyi ba yanzu. Afrah nayi nadamar yin hakan ban zata shagon mu ze k’one ba kuyi hak’uri ina kan neman aiki har yanzu kuyi hak’uri dan Allah.” Afrah bata ce mata komi ba. Jakarta ta zazzage kan gado dan tattara credentials nata. Fitsari ne ya matse ta, bayan ta shige bayi Afrah ta lalimo kan gadon tana duba papers d’in dan ko bata yarda da abinda Fannah tace mata ba nacewa ta yaga card d’in. Kap ta duba bata ga komi ciki ba har ta hak’ura se kuma ta d’au jakar ta, dudduba zip nacikin jakar take can tajiyo takarda tana cirowa taga card d’inne daidai lokacin Fannah tafito “Afrah me kike min da jaka.” “Ya Fannah me wannan?” Da sauri Fannah ta hauro kan katifar ta amshe card d’in, baki ta bud’e wangalau “aina kka samu?” “Ina kuwa? Cikin jakarki? Dama baki yasar ba kenan dan bakisan karb’an aikin ne kika min k’arya kin kyauta.” “Wallahi tallahi Afrah kinji rantsuwan muslumi kenan bansan ya akayi abin nan ya dawo jakata ba aida nansan da zamansa da na kirasa tuni nida ake threatning d’ina kan za'a kaini gun ‘yan sanda?” Shiru tayi tana nazarin wani abu can tace, “aikin Asma’u definately ita tasamin cikin jakata” nan taba wa Afrah labarin komai. _10 minutes later... Dadai k’arfe 5:30PM_ Fannah ce zaune kan kujera d’ayan hannunta katin Anas ne d’ayan kuma wayarta a kunne tana jiran Anas ya d’au wayar. Zuciyarta se bugawa yake bababam! Babam! *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:48, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 2⃣1⃣ Yusuf nada mutunci sosai cikin d’an k’ank’anin lokaci suka saba da juna, dake yanada surutu sekuma gashi shekarunsu d’aya, ma’aikaci ne shima a company’n. Har kitchen d’in ya kaita yajira bayan ta gama had’awa ta bashi ya amshi yakai wa Anas sannan ya dawo dan rakata har waje. wajen wata elevator suka nufa wanda is different from na d’azu dan haka ta tambayesa ko ina zasu. Murmushi yamata sannan yace, “sauk’a zamui zuwa first floor saboda in fita dake kar ki b’ata a wannan babban gini.” Murmushin ta maida masa “amman naga ba tanan muka hawo da Mr. Fauzi ba.” “Hakane, ta private elevator’nsa kuka hauro wannan kuma da zamu shiga shine na public, wancan nasa ne shi kad’ai ke shiga you are lucky ma kinsamu kin shiga wancan.” Ya mata bayani. ‘yar murnushi tayi tabi bayansa har waje ya rakota ya tsara mata napep sannan ya koma ciki. Daga can kasuwa ta wuce ta musu siyayyan abinci sosai tunda sun samu kyauta. Isarta gida keda wuya ta tarar da ‘yan sanda tsaye daga gani ita suke jira fuskar su Mami duk ya jik’e da hawaye. “Yawwa ga ta nan” cewar wata nurse. “Ku tsaya please.” Fannah tace da polisawan. “Dalili?” Cewar nurse d’in. “Ga kud’in kunan nasamu dan Allah” nan ta irga dubu goma ta bata sannan suka fice. Godiya Mami tayi wa Allah da gudu ta ruga tayi hugging Fannah. “Fannah dan Allah kiyi hak’uri ban tab’a san d’aya daga cikin abubuwan da suke faruwa dake su kasance haka ba dan Allah kiyi hak’uri.” “Haba! Mami wace erin magana kike inda kunji good news danake tattare dashi ma da duk kunbar kukan nan. Ga nan siyayya na mana nasamu aiki!!” Atare duk sukace “dan Allah???” “Alhamdulillah.” cewar Afrah. “Aina?” Mami ta tambaya. “A Flames Enterprises wallahi Mr Fauzi ya d’aukeni aiki wai zanna had’asa masa coffee...” nande ta musu bayanin komai. Sosai Mami sunji dad’i musamman ma dasukaji albashinta dakuma kyautan da ya mata. Nasiha sosai Mami tama Fannah dukda cewar tasan Fannah da hankali. Albarka tata sawa Anas data ta tsine masa da a baya. *** Tun k’arfe 4:40PM Fannah ke rik’e da wayarta gudun karta k’ara ko minti d’aya kan lokacin da Anas ya bata. 4:50PM na yi ta kirasa yana kwance kan gado alokacin call d’in yashiga yana gani yagane ita ne beyi picking ba instead seya katse nan yayi saving number’nta da *COFFEE MAKER* cike da mamaki ta sake kira mesa ze katse bayan shi yace ta kirasa be d’aga ba sansa ya kusan tsinkewa. Cike da tsiwa yace “ke baki gane kan aiki ne? Kinga nayi declining call meaning na gane kece kenan haba!.” “I’m so-” bata k’are maganar ba ya katse wayar. Miyau Fannah ta had’e ita kam Allah bata ikon jure wulak’anci da masifan Anas. _Washegari..._ Da safe da misalin k’arfe 7:40AM Fannah da Aiman da Afrah suna kwance kan katifarsu se bacci suke rafkawa an samu an k’oshi jiya wayar Fannah yasoma ringing firgit ta farka dake wayar na k’ark’ashin pillownta a gigice ta d’aga ganin sunan daya bayyana kan screen d’in ya wassakar mata da bacci. *MR. FAUZI* giara muryanta tayi sannan ta d’aga. “Assal-” be jira ta k’are sallaman ba ya katse ta “be here in my office at 8:00AM. Don’t be late” kafin tace “okay” ya katse wayarsa. Ita ba ma wannan ba duban agogonta tayi taga 7:42PM “YA SALAM!!” ta d’anyi ihu “yaushe zanyi wanka in karya in tsari napep in isa har NEW GRA cikin minti 18 wayyo Allah help me.” Ko tafasa ruwan zafin wankanta batai ba da ruwan sanyi tayi wankan anayi ana ihu har ta k’are tafito ko shafa mai batai ba, da k’yar da fad’a da kokuwa tasamu ta kama gashinta hakan ma be kamu ba sakwa-sakwa kawai de aje ne. Tea da biredi ta karya da, ba Butter bale Jam haka gayansa taci ta saka wata maroon material lace da farin hijabi nan da nan ta d’au wayarta tajefa cikin jakarta da d'ari biyar ta fice. Duban agogonta tayi taga 7:53AM ji take kamar ta fire kafin ta sami keke napep har da 55 yayi. A takaice de se 8:20PM ta isa New GRA. Lattin minti ishirin tayi, imagining kalan masifan dazata sha gun Anas kawai take dan sanda ya fad’a mata baya tolerating late coming. Da Yusuf ta fara yin karo shiganta ciki ko gaisuwan arziki bata tsaya sunyi ba ta shige elevator se sauri take yayi ya ruhu, yana ruhuwa kuwa yafara tafiya sama ji take kamar ta fire sama bayan ya bud’u tafita da sauri gudu tayi ta k’arisa bakin k’ofar ta bud’e a hankali ta shiga tsaye ta gansa bayansa na fuakantarta sanye yake dawata pitch long sleeve shirt wanda yad’anyi rolling sleeves d’in zuwa k’ark’ashin elbow nasa. Waya ne rik’e a kunnesa se faman masifa yakeyi fitsari Fannah tasoma ji take tun kafin a fara mata nata bayan ya k’are wayar ya buga wayan kan table d’in tare da jan tsuka. B’ari take tayi “zaki k’ariso nan ne kokuma senayi firing naki!” Ya daka mata wata erin tsawacaccen tsawan da be tab’a mata ba. Tuni hawaye suka ciko idanunta tafiya take k’afafunta suna rawa har ta k’ariso gabansa kanta a k’asa ko fuskarsa bata kalli ba. “Mr. Fauzi dan Allah kayi hak’uri wallahi unguwar danike da nisa daga nan kafin insamu abin hawa har in zo nan-” Katse yayi dawata tsawam sede bekai na d’azu ba “shut up! I don’t care. Koda a wani planet kike bandamu ba in na kiraki you have to be here at the exact time kina jina!?” Hawaye na gangarowa kan kumatunta ta giad’a kai “I’m sorry.” “Wuce ki had’a min coffee make it quick” ya fad’i yana k’ok’arin zama. Kallonta yake sanda takai bakin k’ofa sannan ya tsaida ta. “Ina kuma zakije?” Hannu tasa ta share hawayenta “kitchen.” “Okay, wannan kuma fa? Na kwalya ne shi?” Juyowa tayi ta dawo cikin office d’in tana kallon direction dayake nunawa da yatsansa, coffee machine tagani. “Ban gani bane” tace a hankali. “Banasan surutu get on with it duk abinda kike nema akoi cikin fridge d’incan.” Kai ta giad’a seta tuna da halin sa tace, “toh.” A sanyaye ta k’arisa wajen fridge d’in ta bud’e, kwalb’an giyan data gani ba adadi ne ya mugun razanar da ita. Hannu tasa bibbiyu ta rufe bakinta dan hana ihun dake k’ok’arin fito mata. A razane ta juya tana kallonsa shima kallon nata yake. “Lafiya? Gawa ko jini kika gani ciki?” Kasa fad’in komi tayi har yanzu takasa believing abinda tagani. “Ke! Tambaya nake miki.” Kasa amsa sa tayi nanma sanda ya tashi ya nufo wajen, fisgan murfin fridge d’in yayi ya duba cikin. Nanne yagano giyan data gani ciki ne ya razana ta. Kallo ya watsa mata “acikin rules dana fad’a miki sanda na ce miki banasan shisshigi abinda ya kawo ki kawai zakiyi so get on with it.” Yana kaiwa nan ya koma ya zauna. Da k’yar Fannah ta dawo da hankalinta gu d’aya taciro abubuwan da zata had’a masa coffeen da, tare da rufo fridge d’in duk hankalinta bai jikinta bata ma san me take had’awa ba haka ta kwarara sugar ciki tagama takai masa se mamaki take. Yanzu na miji kyakkyawa kamar Anas amman ya b’ata rayuwarsa da shaye shaye? Meyake nema a duniya? Ga kyau ga kud’i mena shaye shaye? Meyake nema? Me yasa yake shaye shaye? Anas na kai coffeen bakinsa ya sake maidashi cikin cup d’in dan uban sugar ga coffeen datasa ciki yayi yawa. K’aran da glass cup d’in yayi sakamakon fashewan da yayi k’asa ya dawo da Fannah daga duniyar tunanin data fad’a a firgice ta mik’e daga kan kujerar data ke zaune tana b’ari, hannunta biyu dafe kan bakinta se raba ido take. “Meh wannan kika had’a min? So kike diabetes yakamani da zaki d’ura min wannan sugar a coffee?” “Sir dan Allah kayi hak’uri my mind was carried away, zan sake had’a maka kayi hak’uri.” ta fad’a tana b’ari. “Fannah Aleeyu in kinsan you are not ready for this job ki tattara kanki kibar min office, NOW!” Ya daka mata tsawa. Hawaye ta soma yi take. “Mr Anas I’m so sorry dan Allah kayi hak’uri zan sake had’a maka wani” da sauri taje ta tsuguna ta soma tattara broken glasses d’in acikin yin haka d’ayan ya yanke ta sosai a yatsar ta. “Arghhhhhh!!!” Ta saki k’ara a firgice Anas ya taso tare da kama ta da hannunta daga sama da k’arfi sosai ya mik’ar da ita. K’ara ta sake saki se hawaye take ganin yadda jinin jikinta ke d’iga sosai a k’asa. “Bakida hankali ne?” Ya daka mata tsawa. “Kin tab’a ganin ana tattara broken glasses da hannu? Mschww.” Hannunta ya ja da k’arfi ya kaita bathroom ba abinda Fannah keyi se kuka ita ko noticing na mijin daba muharraminta ya kama mata hannu ma batai ba dan azaba. Famfo ya bud’e yasa yatsan nata a k’ark’ashi ruwa na tab’awa ta sakar da ihu “arghhhhhh!!!” Kallonta yatsaya yi se hawaye take wanke mata yankan yayi sannan ya zaunar da ita kan toilet sit. Har yanzu se hawaye Fannah take bayan ya fice da ‘yan mintuna ya dawo da first aid box hannunsa bayan ya d’iga spirit jikin auduga ya gwada d’aga hannunta seta kankame se yanzu hankalinta ya dawo jikinta ta hanasa rik’e hannun nata dan haramun ne. Kallo ya bita dashi sannan yaja tsaki ya finciko hannun nata da k’arfi ya danna spirit d’in kai ihu ta sake saki “arghhhhh!!! Wayyo Allah zaafiii!!!” Be cire ba sanda ya tabbata spirit d’in yashiga sosai. Sannan ya ciro plaster ya b’are ya nannad’a mata a hannun. “Get up!” Yace da ita tana kuka tabi bayansa suka koma cikin office d’in coffeen ta wuce zata had’a masa sabo. “Meh kuma zaki yi can?” Murya na rawa tace, “zan sake had’a maka wani ne.” “Saboda ki sake yanke hannunki koh? A jinki nid’in ina san rik’e hannun ki ne? Mschww” Matsowa kusa da ita yayi ta matsa baya take “be telling me the procedure in had’a.” Haka tana fad’a masa abinda zeyi step by step har ya had’a sede ko daya tab’a nasan be masa dad’i kaman nata ba. Tsuka yaja. “Ba dad’i” ya fad’i a hankali. “Sorry sir me kace?” Tsawa ya daka mata “nace ba dad’i! Damn it!” “Sir! But yadda nake had’awa fa haka kayi.” Juyowa yayi ya galla mata kallo “so kike kiji mesa nawa be kai naki dad’i ba? Ehh? Saboda kin fini iya had’awa saboda your hands are special when it comes to making coffee. Dang it!” Ya buga hannunsa jikin bango wanda ya mugun firgita ta. Komawa yayi kan sofa ya zauna tare da sake necktie nasa. Numfashi ya saki “mik’o min bottle na giya d’aya cikin fridge d’in.” Ido Fannah ta zaro waro waro. Se salati take a zuci. “Bakiji me nace bane?” Ya fad'i a tsawace. K’arya tayi, “na’am banji ba.” “Nace ki mik’o min bottle d’aya na beer (giya).” “Wayyo Allah!” Fannah tace a zuci “yau za’a sha giya a gabana Ya Allah kace da wanda ya sayar da wanda ya raba da wanda yasha duk sunada zunubi. Wayyo ya zanyi?” “Don’t let me repeat myself!” ya fad’i a tsawace. Bata san sanda ta d’auko ta kai masa ba. Fisga yayi ya bud’e tare da yin wulli da murfin daya kafa a bakinsa be cire ba sanda yashanye rabi. Take idanunsa suka soma juyawa wanda ya mugun firgita Fannah wai a ina tasan wannan idanu? Se yanzu ma take k’ara ji a jikinta sun tab’a had’uwa. B’ari take sosai. Bayan ‘yan mintuna ta kira sunan sa “Sir?” Shiru kukeji. “Sir?” Tasake kira “uhmmm” ya amsa a gigin bacci. Gabansa ta k’arisa tasa hannu tana waving a iska ko kad’an be motsa ido ba da alama bacci ya sacesa. Giyan hannunsan ta gwada karb’a ya damke a jikinsa da k’yar tasamu ta karb’e a hankali ta je ta juye a bayi tayi flushing data dawo kuwa ta samesa yana bacci a karkace, kansa yayi gefe guda har ta kai bakin k’ofa zata fita sekuma ta tuna yadda yamata treating ciwonta dukda yata mata tsawa, be kamata tabar sa haka ba shima tabbas inya cigaba da kwanciya haka ze tashi da ciwon wuya komawa tayi ciki dan giara masa kwanciyar, sede bata san ya zatayi ba saboda batasan tab’a sa. Tsayawa tayi kansa tana nazari... *© miemiebee* beenovels.mywapblog. [12:48, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 2⃣0⃣ Ringing wayar yake amman ba response, bayan ya tsinke ta sake gwadawa nan ma haka har ta tsinke Anas be d’aga ba. Anas na kwance kan gadonsa yana ganin wayan na ringing ko yunk’urin d’agawa beyi ba danko baya d’aukan waya within time d’innan inba wai familiar number yagani ba. D’ayar number’nsa ta zuba nanma two missed calls duk be d’aga ba. Anas na gani nanma yak'i d’agawa. Fuksarta cike da disappointment tajuyo ta kalli Afrah. “Afrah be d’aga ba 4 missed calls na masa be d’aga ba. Omg!” Wayarta ta duba taga lokaci pass 5. “Oh no! Se yanzu na tuna sanda yace min kar na kirasa within 5 to 8.” “Toh seki bari se anjiman ai ki gwada.” Kai Fannah ta giad’a mata. **** Sosai Anas yayi missing coffee’n Fannah, bayasan shan komi inba coffee’n Fannah ba. Tun ranan da suka had’u yake jiran kirarta amman shiru. Bayan kwana biyu yaje ya duba coffee shop nasun yaga k’urumus komi ya k’one a tunanin sa wai a ranan ko washegari Fannah zata kirasa ta amshi aikin daya offering mata amman ina har yau shiru, k’ok’arin mancewa da coffee’n yake tunda basamu zeyi ba. Inda kuwa yasa a binciko masa ita da a ranan ze sameta amman kuwa girman kai irin nasa bare barsa ba. Washegari da safe da misalin k’arfe tara bayan Fannah tagama shiri tasaka atamfa ne ja da baki seda bak’in hijabi wanda yamugun sake fidda hasken ta. Ba makeup kamar yadda ta saba, daga kwalli se kwalli da lipgloss a baki ta d’au credentials nata tana shirin fita zuwa company’n Anas tunda bata samesa ta waya ba zataje ta samesa in person. Koda ta sake kiran sa ajiyan around pass 9 be d’aga ba acewarsa wai ko irin mata masu kiran san nan ne danko kirar yayi yawa. Isarta company’n keda wuya. Wannan shine karo na biyu da take sa Enterprise d’in a ido. Bayan tashiga ciki ta tsaya raba ido dan bata ma san ta ina zata fara neman Anas cikin wannan babban building ba, ita bama wannan ba karya ganta ya cicci mata mutunci yanzu danko baida mutunci. Reception ta hango ta k’arisa wajen da fara’arta ta gaishe da receptionist d’in wani kallon bakwai saura kwata ta mata “how can I help you?” Tace da Fannah tana tauna chewing gum bakin nan yasha jan janbaki. “Uhm Mr. Fauzi nazo gani please.” “Mr. Fauzi?” Cewar receptionist d'in tare da d’age gira. “Ked’in zaki ga CEO? LOL” ta k’yalk’yale da dariya. “Eh kwanakin baya ya tab’a offering d’ina aiki yace kan duk sanda na yi making up mind d’ina in zo in samesa. Ki kaini wajensa please.” “Ya sunanki?” “Fannah Aleeyu.” “Kina da appointment dashi ne? Yasan da zuwanki? Is he expecting you?” “Actually no amman in ya ganni ze tuna please ki kaini wajensa please.” “Uhm Fannah kinga Boss d’ina is a very busy man bareyi in kaiki wajensa ba, ba tare da yasan da zuwanki ba in zaki zauna kijira in masa magana yaso ko zuwa gobe ko jibi se a had’a muku appointment seki dawo.” “Ma’am please kiyi hak’uri dan Allah I need this job so badly mahaifina ba lafiya ki taimaka please wallahi ya ganni ze gane ni.” “Fannah kinga kiyi hak’uri ki fice daganan dan nan ba gidan bada taimako bane.” “Ma’am please.” “Security!” Receptionist d’in takira “kuzo ku fita da wannan ‘yar please.” Nan security sukayo wajen suna tambayan meya faru. Daidai lokacin elevator yake bud’uwa Anas ne ya bayyano yana sanye da navy blue suit da blue sunglasses a fuskarsa, gashin nan anyi styling nasa masha Allah, fuskar nan nasa tamk’e ba alaman murmushi. Wani na miji ne a bayansa wanda ga dukkan alamu PA’n sa ne. Taku yake magestically cike da k’asaita yana duba agogon hannunsa da alaman meeting zasa, tafiya yake kai a sama yakaida wajen su Fannah ta kira sunansa “Mr. Fauzi” cak ya tsaya sannan a hankali ya juya ya kalleta ba tare da ya cire sunglasses d’inba. Yana ganinta ya tuna da ita danko kullum seya yi tunanin coffee’n ta ba k’arya yayi missing coffeen nata sosai sosai amman kunsan Anas da girman kai sam ba nuna mata zeyi yayi missing ba. “Good morning Mr. Fauzi.” Fannah ta gaishesa. Security’n ne ke k’ok’arin jan Fannah waje Anas ya dakatar dashi. Ba tare da ya amsa gaisuwar taba “whats going on here?” Ya tambaya authoritatively. Receptionist d’ince ta amsa sa. “Uhm Boss wannan yarinyan ne wai sunanta Fannah Aleeyu that tazo ganinka kuma ni na duba banga kunada appointment da ita ba.” Kallon rainin wayo yake ma Fannah “You’re right banida appointment da ita send her away.” Dagangan ya fad’i hakan danko yasan she is badly in need of the job saboda aikinta data rasa. “Mr. Fauzi please don’t send me away. Na yarda da aikin daka bani koda N10,000 ne zan karb’a please. I’m badly in need of the job na rasa aiki na please Mr. Fauzi.” Shiru yayi kamar wanda bareyi magana ba sannan cikin muryar sa me dad'i yace, “okay so wannan aikin is a second choice to you, sanda kika rasa wancan zakizo nan. I don’t need you yanzu na samu wanda ke had’amin coffee. Take her out” yace da securities d’in. “Mr. Fauzi please I beg of you dan Allah karka korani, I'm badly in need of this job.” Agogon hannunsa ya duha “I will have to think about it yanzu haka inada meeting in zaki zauna kijirani zuwa 12 zan dawo then se inyi deciding ko zan baki aikin ko baran bayar ba.” Wani sanyi Fannah taji a ranta dukda kuwa bawai aikin ya bata ba considering yace zeyi but still she is thankful. “Nogode Mr. Fauzi thank you so much zan jiraka.” Kallon ta yasake cike da rainin hankali sannan ya fice. Harara receptionist d’in ta watsa ma Fannah ita so take kar Fannah tasamu aiki anan da kyantan tannan tsab zata iya juya ma Boss hankali. “Toh ai ba tsayuwa zaki tayi nan ba ga kujeru can sekije ki zauna ki jirasa Allah sa bawai kinzo bane ki mana snatching boss dan ki sani yafi k’arfin ki.” Murmushi Fannah ta mata, “karki damu I have no intention of doing so, kema kin fad’a Boss naku yafi k’arfi na kinga ko ba ruwa da shiga harkansa.” Wucewa tayi ta zauna kan d’aya daga cikin kujerun. Haka tata zama a wajen har tayi bacci ta tashi, har shabiyun tayi Anas be dawo ba. Azahar nayi taje tayi alwala tayi sallah yunwa tasoma ji gashi bata da kud’i. Se k’arfe biyu Anas yadawo wani dad’i taji data gansa shiko yi yayi kamar be ganta ba sanda ya kaida elevator’n ya tura saurayin dake bayan san kan ya kira Fannah. Hijabinta ta daidaita ta d’au jakarta sannan a sanyaye tabi bayan saurayin suna isa bakin elevator’n Anas ya sallami d’an nasa. Bayan ya bud’e elevator’n yashiga Fannah da be gayyace ta ba kuwa ta tsaya tana wasa da dogayen yatsunsa. Tsawa ya daka mata “well? Bara ki shigo bane kokuma se ya ruhu? Kin tabbata zaki iya min aiki kuwa? Banasan ana sani surutu.” “I’m sorry.” Sid’ak ta shiga bada jimawa ba elevator’n ya ruhu. Haka kawai taji zuciyarta na bugawa ita kad’ai da na miji cikin elevator. Ko kallonta ma beyi ba elevator’n na bud’uwa ya fita tana biye a bayansa. Wani card ya ciro yasa a jikin k’ofan office da aka rubuta Mr. Fauzi a sama. Bayan ya bud’u ya shige ciki, itama haka. Suit na jikinsa ya cire ya rataya jikin hanger sannan ya k’arisa kan fankacecen glass table nasa ya zauna kan kujera tare da sakar dawata numfashin gajiya. Kujeran ya nuna mata a hankali ta taka ta zauna. Hijabi ne a jikinta amman sanyi takeji dan yadda Anas ya k’ure AC’n kuma da alama shi bayya ji. “So seda kika rasa aikin ki na can zaki amshi nawa?” Rasa me zata ce masa tayi, ba kallonsa take ba amman tanajin alaman idanunsa kanta. “Have we ever met?” Ya tambayeta dan shima yasoma ji kamar ya tab’a had’uwa da ita somewhere. Take ta d’ago kai suna had’a ido ta kawar da kallonta a garesa sannan ta kad’a kai ai take ta tuna ya hanata using body language. “A’a” ta fad’a murya na b’ari. “Okay So kin karanta catering related course ne a university?” “A’a diploma nakeda a business admin.” “Uhmmm!” ya fad’i yana giad’a kai. “So are you ready to work for me?” “Yes I am” tabasa amsa take. “Nice” yace nanma yana giad’a kai. “Mesa kikazo office d’ina, dana baki card na ce miki nayi ki kirani bawai kizo ki sameni ba.” “I’m sorry Mr. Fauzi amman na kiraka har kusan 4 missed calls baka d’auka ba.” “Saboda kin kira ni time dana ce kar ki kira” ya amsata a takaice. “Ki kiyaye banasan ana sab’a min. So fad’a min nawa kikeson albashin ki ya kasance?” “Sir ni ko nawa kabani muddin be gaza N10,000 ba zan amince.” “Okayyy I will make it N100,000.” Ido wururu wururu ta zaro “N100,000 sir? Gaskiya yayi yawa karya zamo kamar ina cutanka-” Katse ta yayi “kinga da wannan halin bara mu shirya dake ba ko million na yanka miki albashi ba ruwanki bana san shisshigi ki tsaya a inda Allah ya tsaida ke clear?” Miyau ta had’e “yes sir I’m sorry. Nagode.” Hannu ya d’aga da alaman a’a. “Ba’a min godiya. Inada rules sosai in zakiyi aiki a k’ark’ashi na which I have to tell you dan ki kiyaye. Na farko kamar how I told you duk lokacin da nakeda buk’atan shan coffee zan kiraki and zaki bar duk wani abinda kikeyi kizo ki had’a min, clear?” Kai ta giad'a “Yes.” “Good, na biyu banasan shisshigi duk abinda kika gani inba wai nace kiyi magana bane baruwanki aikinki making coffee ne kawai, clear?” Nanma ta giad’a kai “yes.” “Na uku banasan yawan kallo, aiki kikazo yi ba kallo na ba. Ki kiyaye, clear?” Fannah ji take kamar ta k’urma ihu wai mesa wannan Anas yake haka ne? “Clear?” Ya sake tambayanta. “Yy..yes sir.” Ta amsa sa. “Na hud’u ba late coming ko minti d’aya karki k’ara kan time danake buk’atar zuwanki and last but not the least obey all my rules. Nakega for now wannan sun isheki.” “In shaa Allah sir zan kiyaye duka rules naka thank you.” “Kin karya d’aya ready banasan godiya.” “I’m sorry.” “You better be” yace ba tare da ya kalleta ba, duban cikin wasu files dake kan table nasa yake “gobe zaki fara aiki.” Bayan ‘yan mintuna ya d’ago fuskarsa yaga Fannah zaune kan kujerar har yanzu tana wasa da yatsunta. “Well? Me kikeyi har yanzu? You’re dismissed ko komai ne se an riga fad’a miki sekace karatu?” “I’m sorry” tace. So take ta tambayesa alfarma amman kuma tana tsoro kar yace tacika tak’uri da rashin godiya. A hankali ta mik’e har takai bak’in k’ofa sekuma ta kasa fita tasan inba Anas ba bata da wanda zata nema alfarma gunsa ya bata a yanzu, dubu goma take nema ta gama biyan kud’in asibitin Baba. A hankali ta juyo ta k’arisa gaban table nasa ta tsaya ba tare da tace komi ba dan bata san ma ta ina zata fara ba. Sarai yaji tsayunwanta kansa amman yak’i d’aga kai se files dake gabansa yake ta dubawa can da kallon da take masa ya ishesa ya d’ago kyakkyawar fuskarsa tare da kafa blue eyes nasa kanta. Take ta sadda kanta k’asa. “I thought na fad’a miki banasan ana kallonna haka ko?” “Kayi hak’uri” ta fad’a a takaice ba tare data d’ago kai ba. “So me kike min tsaye akai? Ko bodyguard kikeson na baki? Nace you’re dismissed zaki iya tafiya.” “Mr. Fauzi dan Allah kayi hak’uri nasan banida right da zan tambayeka wannan alfarma amman kayi hak’uri please ina buk’atan kud’in ne sosai.” Kallonta yake cike da mamaki. Papers na gaban nasa ya rufe tare da had’e hannunsa biyu k’ark’ashin hab’ansa yana kallonta. “What are you saying? Zo ki zauna” yayi gesturing nata. Bayan ta zauna ta soma kamar haka; “Mr. Fauzi mahaifina ne baida lafiya nagama biyan kud’in magunan sa sauran 10k sekuma na rasa aikina yau kusan sati kenan ‘yan asibitin sunce in ban biya ba zasu iya sueing d’ina court. Please taimakon ka nakeso.” Kallonta yake amman sede wannan karan kallon bana tsiya da rashin mutunci kamar yadda ya saba ba. Duk banzan hali irin na Anas when it comes to family ne yanada tausayi sosai. “Me zan miki kenan?” Ya tambayeta a hankali sekace bashi ba. Ita kanta mamaki question nasa ya bata dakuma yadda yayi tambayar. Kai ta d’ago tana kallonsa cike da mamaki samnan ta kau da kanta. “Acikin salary na nakeso kayi deducting dubu shabiyar kabani please, in shaa Allah zan maka aiki me kyau ba fashi that I can assure you.” Kai ya giad’a a hankali. Drawer’n gefen damansa ya ciro bundle na d’ari bibbiyu da d’ari biyar-biyar ne ciki na d’ari biyu ya ciro tare da rufowa. A gabanta ya ajiye. Ido ta zaro “sir-” Nan ya katse ta “take it, kije ki biya kud’in asibitin mahaifinki dashi Allah bashi lafiya.” “Sir thank you so much but dubu shabiyar ma ya isheni banason in k’arasar da kud’in duka kafin wani watan.” “Ba baki nayi dan in cire daga salary’nki ba nabaki ne a matsayin taimako so you can go now.” Mamaki ne yacika Fannah tama rasa ta ina zata soma masa godiya. “Jazakallahu khairan Mr. Fauzi nagode sosai.” Kai kawai ya giad’a mata dukda kuwa baisan godiyanta. Ta tashi zata tafi ya tsaida ta “before you go inasan ki had’a min coffee.” “Okay sir amman-” Katse ta yayi “just shut up!” Ya daka mata tsawa. Har tsakiyan kanta tajiyo wannan tsawa wai ace yanzu mutum yagama magana da hankali kuma seya soma masifa. Tana kallonsa ya kira wani a waya bayan ‘yan mintuna wani d’an saurayi yashigo. “Yes Boss.” “Uhm Yusuf ka kai ta kitchen ka jirata ta had’a min coffeen seka kawo min kekuma daga can sekiyi tafiyan ki bainda number’nki by 4:50PM ki kirani saboda inyi saving.” “Okay Mr. Fauzi in shaa Allah zan kiraka.” “Allah sa dan in kika manta kika kirani before or after the time a bakin aikin ki. Off you go” nan suka fice tare da Yusuf zuwa kitchen. *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:48, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 2⃣2⃣ Ta kai kusan minti biyu tsaye kansa tana nazarin abin yi, chan ta shiga d’akinsa tafito dawata sweet pillow dashi ta riga tura kansa dashi har sanda ya fad’a ya kwanta kan kujeran da k’afafunsa k’asa. Nanma ta juya zata fice ta sake dawowa, tasan inta barsa haka kunkuminsa ze iya masa ciwo kasancewar kujerar dogo ne, tunanin ya zatayi ta mik’ar dashi take. Ido kawai ta rufe tana “astaghfurillah astaghfirullah astaghfirullah” ta d’aga dogayen k’afafunsa ta ajiye kan kujerar duk se bacci yake me uban nauyi ko jin abinda ake mai baiyi. Takalmansa ta cire masa. Bayan ta koma d’akinsa ta d’auko masa pillow, nazarin ya zata sa kansa kai take amman takasa, ganin ba mahilicci se Allah kawai nan ma ta rufe ido tana “astagfirullah” ta d’aga kansa, lis hannunta yashige cikin wavy long hair nasa me uban laushi, bayan ta aza kan nasa kan pillow’n ya cigaba da bacci abinsa a hankali. Kallonsa ta tsaya yi sam sekace ba shiba in yana bacci, sam bara’a ce shine me masifa da cin mutunci ba, he is looking so innocent in yana bacci. Fita tayi daga office nasan ta sauk’o k’asa can ta hango Yusuf nan ta nufa wajensa yana ganinta ya kira sunanta. “Fannah bade tafiya zakiyi ba?” “A’a” ta kad’a masa kai. “Mr. Fauzi yana bacci.” Ido wuru wuru Yusuf ya zaro. “Bacci? Kin masa wani abu ne?” “Mesa kace haka?” Juyawa yayi left and right ganin ba wanda ke zuwa sannan yace, “a iya sani na Boss baya bacci a office fashe an b’ata masa rai seya sha abinda ya saba sha dan ya gusar masa da b’acin ran.” “Kana nufin haka yake always kullum yana sha?” “Ehh amman kija bakinki kiyi shiru kinga kap nan ba wanda yasan yanayi nima dake abokin k’aninsa ne saisa na sani.” Cike da mamaki Fannah ke kallonsa “amman ko kasan dalilin dayasa yake shaye shayen? Naga ba abinda Mr. Fauzi ya rasa kyau, kud’i mesa zena shaye shaye?” “Shhh! Fannah kinsan in aka ji muna wannan magana firing namu za’ayi. Nide iya abinda na sani shine yanada horrible and terrible past, ance past d’insa ne yasa yake duk wani abinda yakeyi yau, dakuma mutuwan da Babansa Mr. Muh’d yayi a hannunsa. kika lura Boss baya dariya, murmushi ma se in takama.” Kai Fannah ta giad’a nufin tagane inda ya dosa. “Allah sarki amman baka da idea mene ne yafaru a past nasan ko mutuwa wani ya masa?” “A’a Fannah abinda nasani de wai mahaifiyarsa has something to do with it.” “Ayyah” Fannah tace “toh shi be iya rungumar k’addara bane?” “Ai da ya iya da bare na yin abinda yakeyi ba. Kinga lets keep quiet kar a jiyo mu yanzu ayi waje damu.” _3 hours later..._ Da misalin k’arfe 11:30AM zaman kad’aici ya isa Fannah, Yusuf ya wuce 4th floor yana aiki. Tashi tayi daga inda take zaune ta wuce office na Anas a hankali ta bud’e k’ofar dan masa sallama zata tafi. Yadda ta barosa haka ta samesa. K’arisawa tayi ta d’au jakarta dadai tazo fita seta tsaya kansa tana kallonsa tana tuna abinda Yusuf ya fad’i mata nan Anas ya bud’e blue eyes nasa suna had’a ido ta kau da kanta cike da kunya. A razane ya mik’e ya zauna yana tuna abinda ya faru. Kafin tace “ni zan tafi” ya riga ta fad’in “me kikeyi anan?” Baki na b’ari tace “ta..tafiya zanyi nazo d’akuja jakata ne.” “Tafiya zakiyi? Da izinin waye? Wait! Ma tukun” Ya tsaya ya kalli k’afafunsa ba takalmi. A gefe guda yagan su. “Waya baki izinin tab’a ni har kicire min takalmi? Wait wannan pillow fah? Waya baki legal right da zaki d’aga min kai ki aza kan pillow?” “Ss..sir” tayi i’ina “I’m sorry.” “Ina kuma kika kaimin bottle na giyan dake hannuna?” “Sss... sir I’m sorry.” Ta fad’a kanta a k’asa. “Meaning?” Ya tambayeta a takaice. “Na zubar.” “Kin meh? Kinsan ko nawa na saya?” “Kayi hak’uri dan Allah.” “Ba nasan jin komi d’au jakanki kibar min building you are fired.” “Sir plea-” Katseta yayi “Now!” Ya daka mata tsawa. Fannah bata san sanda ta fara kuka ba, “sir dan Allah kayi hak’uri it won’t ever happen again karka koreni please.” “Then ki dena min shisshigi.” “Nadena daga yau dan Allah kayi hak’uri.” Kai ya giad’a mata “you’re dismissed for today tunda hannunki is useless baraki iya aiki dashi ba.” “Sir I can, in had’a maka coffee ne?” Kai ya giad’a mata. Jakarta ta ajiye a yayinda ya zabura yashige d’akinsa to bathroom. Kafin yafito har ta had’a masa ta ajiye kan table bayan ha zauna ya jawo cup d’in yana sha yana aiki a laptop nasa Fannah kuwa kallonsa ta tsaya yi har yanzu maganan Yusuf ya tsaya mata a wuya so take taji mesa yake shaye shaye. Ba tare da ya kalleta ba yace, “the next time kika sake kallona zan koreki daga nan.” Ji tayi kamar ta nitse a k’asa. Da k’yar tayi k’arfin hali tace, “zan iya tafiya?” Ba tare daya amsata ba yacigaba da abinda ke gabansa can Kacallah ya shigo ya kawo masa wasu files yayi signing. “Boss Mr. Nazeef ne yakeson ku had’u dashi akoi wani presentation dayakeson maka regarding project na building drawing d’incan nasan you’ll be busy through out wannan week amman dan Allah consider him na had’a muku appointment tun last 2 weeks yakeson had’uwa da kai.” “Kacallah bareyi mu had’u dashi ba, I will be very busy through out this week kabari ko zuwa next week.” “Boss kayi hak’uri please wallahi dak’yar nasamu na had’a muku please.” Hannu Anas yasa cikin gashinsa yana hargitsawa “ohhh! Kacallah I’m not in a good mood yau please go I’m sorry.” Nan yagama signing wa Kacallah ya fice. Fannah kam mamaki Anas yake bata wai mutum ata had’asa da Allah amman baiji da sauri ta kawar da kanta daga kansa kafin ya koreta. Ana cikin haka wayarsa ya soma ringing nan Fannah ta d’ago kai tana kallonsa bayan ya duba yaga wa ke kira yaja tsaki ba tare da ya d’aga ba. Call d’in na tsinkewa aka sake bugawa a fusace ya d’aga wayar yasoma magana a tsawace “Aleeya please karki sake kira na, wace erin super glue ce ke? nace miki banasan ki I don’t love you ki hak’ura mana! Don’t ever call me again ni na fad’a miki.” Karap ya katse wayar. Baki wangalau Fannah ta bud’e tana kallon Anas dukda cewar batasan meya had’asa da budurwar tasa ba setaji ta tausaya mata aiko ma me tayi bekamata yamata haka ba, yayi hurting feelings nata yayi yawa haba mana. “Lafiya?” Ya tambayeta tare da dawo da ita daga duniyar tunanin data fad’a. “Eh..ehh lafiya” ta fad’i a rikice. “Then stop starring at me, kidena kallo na haka please!” Ya daka mata tsawa. Kuka ta soma take tasa hijabinta ta rufe fuskar ta dashi. Ita dama ya sallameta taje gida tagaji da zama nan. Bayan kamar minti goma akayi knocking bakin k’ofar office na Anas a lokacin kuwa yana kan waya nuni yayi da ido kan Fannah taje ta bud’e. Hawayenta ta gama sharewa sannan ta mik’e taje ta bud’e wani ne bata tab’a ganinsa ba. Bayan Anas ya kammala wayan ya d’ago blue eyes nasa ya aza kan yaron “yes Haruna wani abu ne?” “Boss yanzu wani ya kawo wannan flowers wai daga Aleeya kan kayi hak’uri ga letter nan manne a jiki.” Nan ya matso kusa da table na Anas da nufin ajiyewa. “Ka kuskura ka ajiye wannan gabbage (bola) a gabana you’ll be fired.” Ai tsam Haruna ya rungume flawan a jikinsa. “Boss dan Allah kayi hak’uri.” “Ka fita dashi bana san ganinshi cikin office d’ina.” “Yes Boss. Dama kitchen ne ya d’an kama da gobara amman an samu an kashe da wuri, b’arna kad’an yayi wanda ya kamata a kira me giara da wuri.” Ya fad’a yana b’ari dan ya karanci yau Anas is not in a good mood. “Meya jawo gobaran?” “Chef (me girki) Zainab ce ta manta tabar cylinder a bud’e se gas yayi flowing amman bada sanin ta bane.” “Kaje kayi firing nata now wannan ganganci ne, kace mata inji ni ta tattara kanta tabar min building.” “Yy.. Yes Boss” take ya juya ya fita. Fannah kallon Anas take cike da mamaki mesa zuciyarsa take da tauri haka? “Kinada abin cewa ne?” Ya tambayi Fannah ba tare da ya kalleta ba. “A’a” ta amsa a takaice. Tun k’arfe 2:00PM Anas ya tattara kayakinsa yasoma shirin tafiya gida. Coffee cikin flask yasa Fannah ta had’a masa takuma kai masa har cikin mota sannan ya fice koda ya isa gida Amal kawai ya kula ya wuce d’akinsa. Ba komai ne yasa Anas acting haka ba kuwa a ranan se dan mafarkin Ummimi dayayi. Fannah kuwa isarta gida duk su Mami suka soma jero mata tambayiyi ya sabon aikinta, k’arya tayi tace musu great, alhamdulillah. _Washegari..._ Tun k’arfe 7:00AM Fannah ta gama shirinta dukda kuwa Anas be kirata ba amman dan gudun kar tayi latti. Se 7:30AM ya kirata. Tana d’agawa kafin ta gaishe sa yace, “ina jiranki by 8:00AM in kika k’ara koda minti d’aya a bakin aikinki.” Kafin tace, “okay” ya katse wayar. Daman tagama shirinta kud’in transport kawai ta d’auko ta fice daidai 7:55AM ta isa office kasancewar hold ups. A gigice tashiga ciki ta yi elevator daidai 7:58AM tayi knocking bakin k’ofar office na Anas shiru taji ba amsa tayi knocking kusan sau uku ba response wayarta taciro ta duba agogonta taga har 8:00AM yayi daidai nan personal elevator’n Anas ya bud’u tare da bayyano da Anas. Sanye yake da black suit farin shirt da red necktie sosai yayi kyau. Bayan ya k’ariso ta gaishesa ba tare da ya amsa ba yasa card nasa ya bud’e ko’far tana a bayansa suka shiga office d’in. Jakarsa ya ajiye kan table sannan ya juyo tare da crossing hannayensa kan k’irjinsa yana kallon Fannah dake sanye da jan hijabi da torches na black tanajin idanunsa kanta ta sada kanta k’asa tana wasa da yatsun ta. “Kin karya min doka.” Ya fad’a ba tare da yanuna damuwa ba. A razane ta d’ago kai “Sir wani doka?” “Kinzo nan before time which means kin karya min doka 8:00AM nace kizo nan ba kafin 8:00AM ba. Take not banasan shisshigi next time.” Kai ta giad’a a hankali “okay sir.” “Good make me coffee.” Jakarta ta ajiye kan kujera ta nufa fridge d’in ta bud’e tare da ciro abubuwan da zata buk’ata within 2 minutes ta had’a masa taje ajiyewa kan table d’in amman hannunta se b’ari yake garin haka coffeen ya zube saura a jikinta saura jikin Anas saura kuma kan wasu papers. Tsawa ya daka “WHAT IS WRONG WITH YOU? Meke damunki? Bakida ido ne. Mschww” harara ya watsa mata “you’re so clumsy.” Hawaye take sosai “Mr. Fauzi I’m so sorry dan Allah kayi hak’uri.” Ba tare da ya tanka ta ba ya mik’e a fusace ya shige d’aki tare da bankad’o kofar wanda ya sake razanar da Fannah. Kamar tasan yau ma seya sata kuka ta taho da handkerchief nata danko jiya ta b‘ata farin hijabinta da kwalli. Hawayenta ta share tarasa dame zata goge kan table d’in dan tasan sarai ya dawo ya iske wajen haka ze k’ara mata wata masifan. D’an kwalinta kawai ta cire ta goge wajen. Bayan ‘yan mintuna Anas yafito dawata farar T shirt da ¾ wando wanda ya mugun amsar sa, koda yafito kuwa be tambayeta dame ta goge wajen ba zama yayi kan kujerar. “Me kuma kike jira baki had’a min wani coffeen ba miss clumsy?” “I’m sorry” ta fad’a tare da d’aukan cup d’in se b’ari take ta juya kenan hijabinta yakama kujera take ya sunb’uce daga kanta daman wuyan ya mata yawa. A garin haka ribbon nata data kama kanta sakwa sakwa dashi shima ya fad’i gashinta me uban waya ya bayyana. Take ta tsuguna ta d’au ribbon d’in tana k’ok’arin miyarwa amman dan yadda ta rikice dakuma yadda takejin idan Anas kanta yasa tama kasa kama kan se fad’i k’asa ribbon d’in yake ta mayar da hijabin kuma be zo hankalinta ba. Tunda Anas yake be tab’a ganin gashi kamar na Fannah ba duk zaman da yayi cikin turawa be tab’a ganin erin gashin nan ba ko gashin Ummimi da Amal ma bekai wannan ba. Shi bama tsayin ba uban cikan ne sekace aljanah. Ganin ta kasa kamawa shikuwa ba taimaka mata zeyi ba ya d’au wayarsa ya kira wata. Bayan minti d’aya akayi knocking “come in” Anas yace. Nan wata ‘yar budurwa ta shigo. “Yes Boss.” Da yatsa ya nuna Fannah “help her ku kama mata kanta” cike da mamaki Fannah ta d’ago kai tana kallonsa. Ta rasa gane wani erin hali ne da Anas sometimes seyayi mutunci. “Okay Boss” cewar ‘yar budurwan. Ita kanta gashin Fannah ya bata mamaki sanda ta yi dagaske ta kama mata. “Nagode” Fannah tace mata, murmushi tama Fannah sannan ta dawo da kallonta kan Anas dake d’an rubuce rubuce. “Is that all sir?” Kai ya giad’a mata. “Ungo wannan papers kikai wa Salees ki ce masa ya sake printing yanzu wannan yarinyan ta zubar da coffee kai.” “Okay Boss.” Amsa tayi ta fice. “Thank you” Fannah tace masa. “For?” Ya tambayeta ba tare da ya kalleta ba. “Da ka kirata ta tayani kama kaina.” “Ni bana buk’atar godiyan ki kuma bawai na kirata bane dan ta taimaka miki, ganin gashin kinne banaso.” Har cikin zuciyarta ta ji zafi wannan munanan kalamu amman ya ta iya? Dama shi neman kud’i haka yake. Mik’ewa tayi taje ta had’o masa coffeen wannan karan bata zubar ba. Bayan ya shanye tace, “Mr. Fauzi inasan in d’an fita.” Ba tare da ya kalleta ba yace, “ni ba hana ki fita nayi ba just kisani in na kiraki baki zo a dadai lokacin ba kawai ki tattara kanki kibar min building.” Tasan sarai Anas ze aikata abinda ya fad’i ya korata kamar yadda ya kora wata me girki jiya. Zaman kawai ta cigaba da yi. Kai ya d’ago yana kallonta da blue eyes nasa “well? Kin fasa fitan ne? ” “Eh zan zauna.” “Better” yace ya cigaba da abinda yakeyi. Bada jimawa ba wayarsa ya soma ringing yana ganin Angel ke kira ya d’aga take “Hello my Angel” ya ce. Baki wangalau Fannah ta saki tana kallonsa cike da mamaki. Anas d’in ke kiran wata mace da Angel? Lallai kam koma wacece ita she must be lucky. “Yau ziyara zaki kawo min?... Okay ina jiranki... Oh! Har kin shigo? Toh ina jiranki.” Bada jimawa ba k’ofar office d’in ya bud’u Fannah ta zuba ido tana jiran taga wata babbar budurwa kawai taga d’iyar da k’anwarta ma tafita komi. Da gudu tayi kansa tana masa oyoyo! Zama tayi kan cinyarsa “Ya Anas shine yau ka taho office baka tadani munyi breakfast ba.” “Haba! Angel bacci kikeyi sesa banso tada ke ba.” “Toh ya Anas karka sake kaji? Nifa har yanzu banyi breakfast ba kuma barin yi ba.” “Haba my Angel yi hak’uri. Tare kuka taho da Shettima ba? Kice masa ya kaiki duk eatery’n da kikeso kiyi breakfast in na dawo zamu fita tare.” “Yeyy! Ya Anas” tayi hugging nasa “I love you.” “I love you too Angel.” Fannah harda d’igan miyau dan mamaki wai Anas ke dariya yau haka? Bama murmushi ba? Kuma ba k’aramin kyau dariya ke masa ba ga dimple ga fararen hak’wara. Kallonsu ta tsaya yi yadda suke kama nema yasake burgeta. *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:48, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 2⃣3⃣ “Ya Anas wace wannan tamin kyau.” Cewar Amal da suka had’a ido hud’u da Fannah dake ta kallonsu. “Wannan?” Ya nuna Fannah. Kai ta giad’a “ai kin fi wannan kyau Angel.” Fannah dake murmushi take yanayinta ya soya jin abinda Anas yace. “Dagake Ya Anas?” “Sosai ma Angel wannan ai bata da kyau.” “To Ya Anas wace ita? Metakeyi anan?” “Nima bansanta ba tana aiki anan ne.” “Nikam tamin kyau Ya Anas.” Nan ta mik’e daga kan cinyarsa ta nufo wajen Fannah. “Hi” tace da ita. Fannah na murmushi tace, “hello beautiful.” Amal ta murmusa sosai “dagaske ina da kyau kamar yadda Ya Anas yake fad’i?” “Sosai Ya Anas naki beyi k’arya ba.” “Toh me sunanki?” “Fannah kekuma fah?” “Amal amman Ya Anas na kira na da Angel.” “Nice name Amal.” “Amal kije kiyi breakfast kinji? Karki biyeta da surutu kinji Angel d’ina?” “Okah Ya Anas, Fannah ba-bye.” “Ba-bye” Fannah tamata sannan ta fice. Ita ina ma yadda halin Amal ke haka halin Anas yake dataji dad’i, kawai se tana murmushi wa kanta. “Kuma murmushin me kike?” Babu ta amsa sa a takaice. Kallo ya watsa mata sannan yaci gaba da abinda yakeyi. Coffee sau uku ta had'a masa a ranan sannan da yazo tafiya ta had’a masa cikin flask kamar jiya. **** Fannah da Afrah ne zaune tsakar sede kallo d’aya Afrah tamata tagano Fannah ta wula duniyar tunani. “Wai Ya Fannah tunanin me kike haka?” “Aww ni!” Ta fad’i a birkice. “Ba komai.” “Oh common kidena min k’arya dan Allah. Bade kema kin kamu da san Mr. Fauzi ba?” “Ya Salam!!! Afrah wai giya kike sha ne?” “Toh fad’a min tunanin me kike?” Numfashi Fannah taja, “kinsan wani abu ne Afrah?” Kai Afrah ta kad’a Fannah ta cigaba; “ni al’amarin Mr. Fauzi mamaki yake bani kinsan ban tab’a ganinsa yana dariya ba ke ko murmushi bayya yi kullum cikin masifa da tsawace mutane yake, amman yau da wata k’anwarsa tazo bakiga yadda yake dariya ba wallahi-” Afrah ta katse ta “sekuma ya miki kyau kikaji dama kema yana miki dariyan koh?” “Ke Afrah anyi mutum wallahi.” “Nama fasa baki labarin.” cewar Fannah. “A’a yi hak’uri Ya Fannah please.” Fannah ta cigaba, “kinsan wani biggest secret nasa kuma?” Kai Afrah ta kad’a mata. “Dan Allah karki fad’awa kowa, Mr. Fauzi yana shaye shaye.” “Iyye!” Afrah ta zaro idanu waje. “Yana mene? Shaye shaye fa kikace?” “Ke da Allah kiyi a hankali kar a jiyo mu. Yana shaye shaye amman kuma danayi tambaya se akacemin wai yanada horrible past, akoi abinda ya tab’a faruwa a rayuwarsa can baya wanda yasa yake duk wani abinda yakeyi yau kuma kinsan the most interesting part of it? Duk tsiyar Mr. Fauzi wallahi when it comes to family yanada kirki sosai kiga yadda yabani bandir na N200 mana.” “Gaskiya ne amman Ya Fannah wallahi tausaya miki nake, shaye shaye fa in randa ya bugu ya miki wani abun fah? Ki nemi wani aiki please banasan abu ya tab’a ki.” “Karki damu Afrah in shaa Allah ba abinda ze min, ni so nake naji me tarihin sa mesa yake shaye shaye. No offense amman Mr. Fauzi kyakkyawan namiji ne da duk macen data gansa (musamman ‘yan matan miemie bee novels group LOL) zataji tana sonsa kotaji ya burgeta ga kyau ga kud’i ga class ba abinda ya rasa mesa zena shaye shaye? Dole da akoi k’wararren reason and I must find out wayasani ko in giara masa rayuwa.” Cike da mamaki Afrah ke kallon Fannah, yaushe rayuwar mutane ya soma damun Fannah’n da bata shiga cikin jama’a. Ahhh! gaskia Mr. Fauzi ya k’ure ta fannin had’ewa. “Toh kekuma tanan kika b’ullo yau? Ai bari ya cigaba da saki kuka ni ba ruwa na. Ina ruwanki da shaye shayensa yaga dama ya dawwama dashi mana. Nikam gaskia ina ji miki tsoro.” “Worry not Afrah.” Washegari ma tun 7:00AM Fannah tagama shirinta se jiran call daga Anas take amman shiru 7:30AM nayi kawai ta tsari napep ta k’arisa office nasa koda datayi knocking bakin k’ofar kuwa ba response ta gwada bud’ewa ma a rufe waje ta nema ta zauna daga gefe tana jiran dawowansa. 8:00AM on the dot k’ofan elevator ya bud’u Anas ya bayyana daga bayansa. Cike da mamaki Fannah ke kallon Anas dake sanye da suit as always. Wai shi jira yake ne se takwas d’in daidai ya cika ya shigo a’a kokuwa kawai perfect timer ne? Binsa da kallo take tana wannan nazari har ya iso bakin k’ofar bata sani ba. “Incase kina mamakin ko tsayawa nake se daidai 8:00AM yayi nake iso nan toh you are mistaking kuma wai ban hanaki kallo na haka ba?” “I’m sorry” ta fad’a a kunyace. “Ba abinda na tambaya ba kenan.” “Ka hana...” Ta fad’i kanta a k’asa. “Then kidena, saboda ke barin fara sa niqaf ba. Mschww!” nan ya bud’e k’ofar office d’in yashiga, Fannah na biye a bayansa. Bayan ya ajiye jakansa ya juyo tare da crossing arms nasa a chest nasa yana kallonta. “Waye ya gayyace ki nan?” Sam bata fahimce sa ba. Hijbanta me hula ta sake ja tare da rufe mata kusan rabin fuskarta, ta tsani taji wannan blue eyes nasa kansa. “So kike na sake repeating kaina?” Ya sake tambayarta yana mata wani erin kallon rashin isa. Murya ciki ciki tace, “Sir ban fahimce ka ba.” “Dama ina zaki fahimta? Uban wa ya gayyato ki nan yau? Ni na kiraki nace kizo?” Kai ta kad’a masa “Sir naga yau thursday ne kuma ranan aiki ne shiyasa.” “So what? Nifa sanda na fad’a miki banasan shisshigi, wai ku mata duk haka kuke ne? Tunda kin kawo kanki off you go, make me coffee. Kuma wannan fuskarki da kike rufewa ki bud’e is not as if I’m interested in looking at it.” A hankali ta mayar da hijabin daidai sannan taje ta ajiye jakarta ta had’o masa coffeen yauma sauran kad’an ta sake zubarwa. “Wai wace erin clumsy mutun ce ke? Ehh? Am teilling you yau da wannan coffee ya zube kan wannan building drawing sekin re drawing min I don’t care baki iya ba. Mschww!” fisgan cup d’in yayi daga hannunta wanda a garin haka ya tab’a mata yankanta dake kan warkewa. K’ara ta sakar amman ko a kwalan rigarsa komawa tayi ta zauna kan kujera tana kuka. Anas be ma san tanayi ba can da kukan ya ishesa yace, “ke!” A hankali ta d’ago jajayen idanunta ta a zasu kansa. “K’aran kukan nan na distracting d’ina ko kiyi shiru kokuma ki fita.” A hankali ta mik’e ta sauk’o k’asa inda ta saba ganin Yusuf yau ma can ta samesa. “Fannah ya haka idanunki duk sunyi ja? Kin ji ciwo ne.” Murmushi ta k’irk’iro “a’a ba komai.” “A’a da akoi komi keda Boss ne?” Kamar ta masa k’arya sekuma ta fad’i gaskia kawai. A hankali ta giad’a kai hawaye na sake cikowa idanta. “Haba! Fannah I thought you were a fighter, ai in kikace zaki biye wa Boss kullum kina cikin kuka kenan, haka shi yake in ya bak’anta wa mutum rai ne yake jin dad’i, hak’uri zakiyi kina basa uzuri, wallahi kina ganin Boss haka ne he is weak kawai pretending yake to be strong, past d’insa kullum bibiyarsa yake zuwa present kinga ko dole yana sauk’e haushinsa kan mutane. Kiyi hak’uri.” “Toh amman Yusuf mesa duk tsiyarsa naga yafi wa mata kan maza mesa?” “Nima bansani ba Fannah wannan lamari se Allah. Barinje inyi arranging wad’annan a file room.” “Muje tare ba abinda nakeyi nima.” Haka duk inda ze je Fannah tana biye dashi, sosai ta zagaya building d’in ranan floors kad’an ne batayi exploring ba. Duk wani walak’anci erin na Anas ma ta manta dashi se enjoying kanta take gun Yusuf gashi da surutu da kayan ban dariya. Abinci ma tare sukaci bayan sunyi sallan azahar tama manta yakamata taje ta had’a wa Anas coffee tunda azahar tayi. Anas na zaune kan table nasa bayan ya idda sallah se zanen building drawing d’in yake. Bayan ya gama ya soma modeling zanen, zane ne me uban kyan gaske, bungalow ne amman had’ade harda underground ga garden da swimming pool ba abinda babu ciki. Jiran Fannah yake tun d’azu tazo ta had’a masa coffee amman shiru, shi yanzu ya saba inbe sha coffeen Fannah ba baijin dad’i. Inde ze sha coffeen ta kuwa be damuwa da cin abinci. Har to 1:30PM Fannah bata dawo ba. Wayarsa ya ja daga kan table ya yayi scrolling kan contact nata ya kira to his suprise waya ya soma ringing cikin office d’in wato ko fita da wayartan ma batayi ba. Tsuka yaja yayi hanging take ransa ya b’aci Kacallah ya kira ko ya ganta sam Kacallah yace besa ta a ido ba. Ya kira kusan mutane uku duk ba wanda ya ganta, kokuma suce d’azu sunga wucewarta. Yusuf ya kira daga k’arshe. “Hello Boss?” Cewar Yusuf. “Kaga Fannah?” Anas ya tambayesa ba wasa cikin muryarsa. Tunda Fannah taji Yusuf yakira Boss taji cikin ta ya rud’e. Kai take kad’a wa Yusuf kan yace batta nan amman inaaa shima Yusuf d’in tsoro yake kar Anas ya gano gaskia yayi firing nasa. “Yes Boss.” “Ina take then?” Anas ya tambaya almsot kamar masifa. “Mu.. Muna tare Boss.” “Aikin daka koma yi kenan ko? Toh kaji kasani nan ba wajen baza soyayya bane zaku iya yin abunku a waje amman banda cikin building d’ina.” “I’m sorry Boss it will never happen again.” “Better” cewar Anas “ita kuma budurwar taka kace mata tazo ina jiranta.” Ding! Ya katse wayar kafin Yusuf ya masa bayani, sam ya kasa kallon Fannah. “Yusuf meyace?” ta tambaya duk ta rud’e. “Karkiyi kuka please, kije yana kiranki kinyi wani laifi neh?” “Innalillahi!” Nan ne ta tuna bata had’a masa coffeen rana ba. “OMG! Mr. Fauzi zeyi ball dani yau wallahi coffeen sa na mance, nashiga uku” take ta soma cin faratun ta. “Don’t panic kiyi sauri kije kafin ya sake fusata.” A sanyaye ta mik’e k’afafunta se b’ari suke. Koda ta isa sama kasa knocking tayi bakin k’ofar already hawaye ma sun fara ciko mata a hankali tayi knocking sau d’aya shiru be amsa ba kuma sarai yaji nan tayi na biyu. “Come” yace a hankali ta bud’e k’ofar ta mayar a nitse sannan ta tako cikin office d’in ta tsaya da kanta a k’asa. Pencil dake hannunsa ya ajiye ya d’ago kai yana kallonta. “D’au jakarki kibarmin building” ya fad’i ba tare da nuna damuwa ba. A razane ta d’ago kai hawaye na bin kumatun ta “Mr. Fauzi I’m so sorry dan Allah kayi hak’uri please.” “Don’t let me repeat myself. Kin jini ki d’au jakarki ki tafi zan kira Adam ya biyaki kud’in ki. Now off you go.” Kuka take sosai in Anas ya koreta bata san ina zata samu wani aikin ba yadda neman aiki keda wuya “Sir please, hakan bare sake faruwa ba dan Allah kayi hak’uri.” Ko sauraranta baiyi “in kika barni na sake nanata kaina ranki ze b’aci.” “Sir dan Al-” Yi yayi kamar ze tashi. Har k’asa Fannah ta durk’ushe tana kuka “dan Allah kayi hak’uri wallahi in kayi firing d’ina bansan ina zan sake samun wani aikin ba, ni nake kula da family na Baba na bashida lafiya have mercy please.” Yana jin ta ambato family’nta seya nemi fushinsa ya rasa “get up” yace mata. A nitse ta mik’e tana share hawayenta. “For your family’s sake, zan barki ki cigaba da aiki anan.” Wani sanyi taji a ranta “thank you sir thank you so much.” “Inba wai na manta bane na hanaki min godiya.” Duk wannan magana dayake bai kallin Fannah. Se a yanzu ne yad’ago kai yana kallonta da blue eyes nasa. “Ki bud’e kunnuwanki dakyau ki jini.” Kai ta giad’a “inaji Sir.” “Yau shine na farko kuma na k’arshe da zaki sake zuwa wani waje kibar min wayanki a office kina jina?” A hankali ta giad’a kai. Ya cigaba “kin ajemin saboda in miki recieving calls ne?” “A’a kayi hak’uri.” “Ai dama saboda na hak’uran ne saisa kike tsaye cikin office nan har yanzu. Secondly, building d’ina ba wajen yin hira da saurayi bane in keda saurayin naki kunasan spending time tare seku bari in kun bar nan banasan iskanci cikin nan aiki ya kawo ku ba soyayya ba. I hope am clear.” “Sir Yusuf fa ba saurayi na bane ka-” ta fad’i kanta na kallon k’asa a yayinda ya katse ta “ban damu ba koda mijinki ne, nide na fad’a miki the next time kika manta abinda ya kawo ki nan saboda hira ya miki dad’i you will be fired for good.” Da hannu ya mata nuni wuce ki had’a min coffee. Bayan ta had’a masa ta ajiye kan table d’in. Sosai model dayake had’awan ya mata kyan bala’i sarai ya gane abinda take kallo kenan. “Cikin rules naki I made it clear banda shisshigi so mind your business please” “I’m sorry” tace sannan ta koma ta zauna tare da ciro wayarta tana game ita ta k’osa ma lokacin tashinsu yayi ta tafi gida. Tana cikin yin game a wayarta Anas ya buga table da k’arfin daya firgita ta. “Kashe game d’innan” ya fad’i ransa b’ace. “Sir I’m sorry amman fa nasa a silent.” “Meaning baraki kashe ba kenan?” “A’a zan kashe” ta amsa a takaice. “Then make it quick.” Nan ta kashe daidai lokacin wayarsa ya soma ringing ganin Amal ke kira ya murmusa kallonsa kawai Fannah take. “My Angel” ya ce da Amal. “Ya Anas zan taho office naka yau tunda banje school ba.” “Angel amman fa bakida lafiya kikace.” “Toh Ya Anas ni banasan physics d’innan kuma har double muke dashi yau sesa nayi k’arya.” “Angel! K’arya!” Yayi exclaiming. “I’m sorry Ya Anas.” “Toh karki sake.” “Ya Anas inzo? Inasan inga wancan Fannah d’inne I want to be friend with her.” “Da Fannan?” Ya tambaya cike da mamaki. Jin an kira sunanta ta d’aga kai ta kallesa shima kallon nata yake take ta kau da kai. “Eh Ya Anas ita tabada hankali.” “A’a Angel, Fannah bata zo office ba yau kibari se watarana.” Cike da mamaki Fannah ta d’ago tana kallonsa toh in ba’a office take ba ina take? “Yawwa ba-bye” yayi hanging. Ko kallon Fannah ma beyi ba yacigaba da yin abinda yake. *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:48, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 2⃣4⃣ Haka ta ta zama shiru game dayake sata nishad’in ma Boss nata ya hana ta yi. Time-to-time take satan kallonsa dan ba k'arya model dake gabansan ya bala’in mata kyau. Kafin lokacin tashin su yayi as usual ta had’a masa coffee cikin flask takai masa har mota. Isan Anas gida keda wuya ya wuce d’akinsa thank god Amal bata nan sunfita da Ummie da ta cika masa kunne da surutu bayan ya watsa ruwa ya sha coffeen sa sannan ya kwanta. _Bawan Allah ka cuceni, ka rabani da budurcita martaba ta, ka cuceni barin tab’a yafe maka ba. Kuma ina nan kusa da kai INA TARE DA KAI..._ Firgit Anas ya tashi daga mafarkin dayake yana nishi sosai, ga wani uban zufan dake k’eto masa. Hannunsa bibbiyu yasa cikin gashin kansa yana hargitsawa daidai lokacin knock yazo daga k’ofar d’akin. “Waye ne?” ya tambaya. “Shettima ne in shigo?” “Eh” ya amsa a kasalance. Shettima na ganinsa ya gane mafarki yayi wajen dispenser ya nufa ya d’ibo ruwa ya kai masa bayan Anas yad’an sha ya masa godiya. “Mafarkin wa kayi kuma? Ummimi?” Kai Anas ya kad’a masa. “Shettima yarinyan... *_TANA TARE DA NI_* I can feel it help me find her please. Wallahi shekaran jiya ma sanda nayi mafarkinta kuma it hurts me alot in naji tana cewa na cuce ta na rabata da budurcinta.” Kafad’arsa Shettima ya dafa “Ya Anas kai yanzu koda ka sameta me zaka mata? Kafa riga ka b’ata mata rayuwa” “Shettima I will seek for her forgiveness, zan nemi gafararta koda kuwa kneeling zanyi gabanta I will do it. A rayuwa inasan in karya wa mata zuk’atansu amman bawai in raba su da martabarsu ba Shettima.” Ya fad’a a hankali cike da damuwa kamar ba Mr. Fauzi da muka sani ba. “Toh Ya Anas what if tace bara ta yafe maka bafah? Tace sede ka aureta ofcourse kasan kowace mace zata so kasancewa matarka.” “I will do it Shettima inhar aurenta zesa ta yafemin zanyi, baraka gane yadda abin ke damuna ba.” Sosai Shettima yasha mamakin jin kalman ‘aure’ fitowa daga bakin Anas gaskia Anas yayi regreting abinda ya aikata yakamata yarinyan ta yafe masa duk sanda suka had’u. Kwanciya yayi jikin Shettima a yayinda shikuma ya dafa hannunsa kan kafad’arsa. “Karka damu I’m sure duk rananda kuka had’u zata yafe maka, ni da kaina zan mata explaining komai.” “Thank you” Anas ya ce masa tare da tasowa daga jikinsa ya kishingid’a jikin gado. “Toh zan wuce d’akina Ya Anas please karka sha wani abu, shaye shayen nan da kake ba shi ze warkar maka da tunanin yarinyan nan ba.” Kai Anas ya giad’a masa danko shi yasani sarai in be sha syrup nasa kokuma giya ba damuwansa barasu gushe ba. Shettima na fita shima ya sa kaya ya wuce paint house nasa(d’an k’aramin gida) acan ya bud’o fridge ba komi bane aciki inbanda kwalban giya masu tsadan gaske d’aya ya zaro daga ciki ya nemi waje ya zauna, ya kashe wayoyinsa tukunna yadda bara ma a damesa ba. Sannan ya shanye fiye da rabi. A hankali matsolilinsa suka soma gushewa har se sanda yajisa problem free daga nan ya samu ya kwanta yayi bacci sosai daga kan kujerar ma ya gangaro k’asa ya cigaba da baccinsa se can bayan isha Anas ya tashi nan ya biya sallolinsa. Yayi frying omalet yaci sannan ya k’are kwalban d’azu ya koma ya kwanta. Agida kuwa hankalin kowa ya tashi gashi in sun gwada lambobinsa duk bame shiga gashi kuma ba wanda yasan da zaman paint house daya saya wanda yake zama ciki if he wants to be alone ko Shettima ma besani ba. Shide Shettima yasan sarai yanzu wansa is somewhere yana shaye shaye abinsa. Sosai shaye shayen d’an uwansa ke damunsa shi da yasan ina ze samu yarinyan da Anas ya tab’a raping da ya nemo masa ita, atleast suka had’u hala Anas ya rage shaye shayensa. Ba shi ya tashi ba se washegari da misalin k’arfe 9:30AM ko sallan asuba beyi ba. A gigice ya fad’a bathroom yayi alwala yafito yayi sallah sannan ya koma yayi wanka ko breakfast beyi ba kaya kawai yasa ya d’an gyara gashin kansa ya fice. Driving yayi da sauri cikin d’an k’ank’anin lokaci ya isa office yunwam uba yakeji ko breakfast beyi ba amman bedamu ba saboda zesha coffee. As usual yana shiga aka soma bisa da gaisuwa kai kawai yake giad’a musu har ya isa bakin office nasa can yaga su Kacallah sunyi layi kafin suyi magana yayi apoligising “I’m sorry na makara ne.” “Ba komai Boss tunda kasamu ka fito.” Layin kap yabi da kallo be ga Fannah ba to kode dan be kirata bane yasa bata zo ba yau? Amman ai kuma jiya ma be kirata ba kuma tazo maybe ko tana wajen Yusuf. Bayan ya sallamesu Kacallah da k’yar ya kira Yusuf dan yunwa. Sam Yusuf yace be sa Fannah a ido ba. **** Fannah kuwa yau baccinta tasha ba ita ta tashi ba se kusan to 9:00AM dad’i takeji yau Anas be kirata ba nufin bai buk’atar ta kenan. A dad’inta yau bara a sata kuka ba dan kuwa Fannah zata iya jure wahala da walak’anci amman banda masifa daga an mata masifa take soma kuka, Anas kuwa aikinsa kenan kullum masifa. Sun gama breakfast da d’anwanke se santi suke ita da Afrah suna zaune a d’aki Aiman ta tafi makaranta. “Afrah tashi muje mu gaishe da Baba naji Mami tace ya tashi.” Atare suka shiga d’akin Baba da Mami suka samesa a kishingid’e yana kurb’an tea. “Ina kwana Baba?” Suka gaishesa a tare. “Lafiya emmata na, Fannah ya gajiya kuma?” “Ba gajiya, Baba ya jikinka?” Nan Afrah itama ma ta tambayesa. “Da sauk’i sosai. Fannah Allah cigaba da miki albarka ya k’ara bud’i mungode sosai.” “Kai Baba dan Allah godiyan me haka?” “Shine ai Baba” cewar Afrah “ai nima banje makarantar bane da senayi fiye da Ya Fannah.” D’an dariya Baba da Fannah sukayi, hira kad’an suka tab’a se sanda Mami ta shigo suka fice zuwa d’akinsu. “Ya Fannah are you sure yau bara kije office ba?” “Eh mana ai be kiran ba gashi har goma da mintuna aka, baya buk’atan coffee yau.” “Allah sa!” Afrah tace. “Me kike nufi?” Fannah ta tambayeta a takaice. Wayar ta ta mik’a mata “duba nan kiga.” “Innalillahi! Na mutu!” Fannah tayi exclaiming. “4 missed calls?? Yau Mr. Fauzi zeyi ferfesu na.” “Akan wannan pointless suratan da kike ba gomma kin kirasa ba.” “Afrah wallahi baran iya ba balbale ni zeyi da masifa.” “Oh!” Afrah ta saki numfashi “Ya Fannah yanzu kuka kike? Ai yaci ace kin saba da masifa tun gun Baffa Khaleel. Ki kirasa.” Kai Fannah ta kad’a, fisgan wayan Afrah tayi aiko ta soma dialing number’n Mr. Fauzi. “Afrah in kinayi wa Allah ki kashe tun kafin ya shiga dan Allah, wallahi zan kirasa ki kashe dan Allah.” Ai wayar na nuna an d’aga Afrah ta wurga wa Fannah wayar tayi bakin k’ofa jiran kallon drama tana dariya. B’ari Fannah take ta kai wayar kunne nan ma takasa fad’in komi, kamar yadda shima Anas d’in yayi shiru ransa b’ace se tafasa yake. “Hello Mr. Fauzi.” Tayi managing ta fad’a cikin murya me rawa. Cike da tsiwa yake maganar. “Se yanzu kika ga damar magana? Eh?? Me kika maidani? Toy abin wasa? Wayyo!” Ya saki k’ara tare da rik’e cikinsa dan yunwa. “Mr. Fauzi I’m sorry dan Allah kayi hak’uri.” Ta fad'a idanta na cikowa da hawaye. “Meya hanaki zuwa office yau?” Ya daka mata tsawa. Kuka take kam yanzu. “Si..sir naga jiya danaje baka kirani ba kace na dena ma shisshigi sesa banzo ba ya-” bata k’are maganar ba ya katse ta. “Nonsense na baki nan da 20minutes be at my office” karap ya katse wayar. Hannu Fannah tasa tana share hawayerta a yayinda Afrah ta k’ariso ta zauna kusa da ita. “Haba mana Ya Fannah wallahi kidena masa kuka ze raina ki.” “Da Allah rufa min baki ba duk ke kika jawo ba, ba abin na ja miki Allah ya isa ba.” “Yi hak’uri Anty babba, meya ce miki?” Harara Fannah ta galla mata “bansani ba muguwa kawai.” Nan ta mik’e ta canza kaya ta sako red hijabi tare da jan jakarta ta fice. Afrah na mata Allah kare ma ko kulata batai ba. Bata sha wahala ba tasamu keke napep sede hold ups daya rik’a rik’e su a hanya. A takaice de lattin minti 5 tayi. Duk yadda tayi tabar b’ari takasa. Se addu’o’i take ta suburbud’owa Allah kare ta daga sharrin masifan Boss nata. Knocking tayi bisa k’ofar “come in” yace. Bayan data shigo tagansa yana attending wasu mutane kanta ta sunkuyar tajira har se sanda ya sallamesu. Kallonta yake bema san me ze mata ba chan yace. “In nache you are fired zaki ga laifi na?” Kai ta kad’a a hankali fuskarta na kallon k’asa se b’ari take. Table d’in ya buga da k’arfi a tsorace ta d’ago kanta tana hawaye. “Ban kuma hanaki min magana da body language ba?” “Ka hana” ta fad’i tana share hawayenta. “Na farko yau dagangan kik’a k’i zuwa office kika bar ni da yunwa, na biyu dana kiraki har 4 missed calls baki d’aga ba saboda kin mayar da Boss naki sa’an wasanki.” “Kayi hak’uri dan Al-” Katse ta yayi a tsawace “ban baki izinin magana ba so shut up!” Hawaye se gangara suke kan kumatun ta tana sharesu “na uku da kika kirani back kika k’i magana se sanda kika ga dama. Na hud’u kikayi latti akan latti. Zakiga laifi na in nace na koreki daga nan? Am talking to you!” Ya k’ara mata wata tsawan. Hak’urin ma takasa basa se kuka takeyi shark’af shark’af. “Baraki amsa ba kenan?” “A’a I’m sorry” ta fad’a da k’yar muryarta na rawa. “Kuma kinsan me? Wannan kukan da kikeyin ba damuna yake ba, koda zaki tsiyaye hawayen ki tas barin damu ba, gara kiyi saving nasu kuma har yanzu tsaye kike?” Kai ta d’ago a hankali “a’a” nan ta wuce ta had’a masa coffeen bayan ta ajiye masa coffeen ta juya zata fice kenan ya finciko ta da hijabin ta da mugunta wanda sanadiyar haka ya shak’e mata wuya k’ara sosai ta saki take ta soma kuka. “Nan gaba zaki sake nanata abinda kikayi yau. Mschwww!” Bata ce masa komi ba jakarta kawai ta d’auka ta fice sam yi yayi kamar be ganta ba. Data sauk’o ma tana jin Yusuf na kiran sunanta ta sharesa k’ofa na bud’uwa ta fice bayan ta yabi da gudu Allah ya so ba keke napep a lokacin tsaye take tana hawaye tana kuka me d’an k’ara isowan Yusuf wajen yace, “Haba Fannah mene yafaru ina ta kirarki kika yi kamar bakiji niba. Wani abu ne?” Batace dashi komi ba se kukan da takeyi. “Fannah meya faru kike kuka haka?” Ya tambayeta cike da tausayi. Kukan take har yanzu kamar ‘yar yarinya tayi covering fuskarta da hannu. Hijabinta yaja a hankali ya zaunar da ita kan wata bench. Be sake ce mata komi ba har se sanda ta gama shan kukanta. “Fannah zaki iya fad’amin meya faru?” “Ni nabar aiki a nan.” tace tana share hawayenta. Cike da mamaki yace, “ban gane kinbar aiki ba Fannah kinsamu wani aikin ne?” “Ban samu ba amman zan shiga nema.” “Mesa Fannah, na miki wani abu ne?” “Baka min komi ba amman Boss naka yamin. Yusuf niba mutun ce me neman magana ba, nayi hak’uri da erin abinda Mr. Fauzi yakemin, I can’t take it anymore wallahi ko kashi bara’a masa abinda Mr. Fauzi kemin ba neman kud’in ba hauka bane. Ni kawai ya biyani kud’in ‘yan kwanakin dana masa aiki zanje in nemi wani.” “Fannah kibar magana, nasan you don’t mean what you are saying. Kinsan yadda neman aiki keda wuya ki hak’ura, sekace ban fad’a miki matsalan Boss ba? Haka yake inya k’untata wa mutum ne yakejin dad’i kiyi hak’uri. Yanzu har kika bar aikin nan baki sami wani bafah? Dame zaki biya kud’in magamunan Baba. Kiyi hak’uri.” “Kana nufin in cigaba da aiki k’ark’ashin Mr. Fauzi kullum yata cin mutunci na yana masifeni?” “Ba abinda nake nufi ba kenan. Abinda nake nufi shine ki k’ara hak’uri, ki cigaba da wannan d’in kina neman aiki nima in shaa Allah zan tayaki. Kinga in muka samo miki seki bar nan d’in amman karki bar nan bakida wani aikin please.” Shiru tayi na d’an lokaci “you are right Yusuf nagode sosai.” “Always... Mushiga daga ciki kinji?” Kai ta giad’a masa suka dawo ciki tare. Duk inda zasa tana biye dashi. Seda azahar yayi ta koma office na Anas knocking tayi yace, “come in.” Bayan ta shiga ko kallonsa batayi ba ta zarce ta had’a masa coffee. “Na d’au kinbar aikin ne ai.” Yace da ita yana daddana laptop. Nanma shiru ta masa ta fice ba ita ta sake dawowa ba se to 4 ta had’a masa coffeensa cikin flask ta d’auka takai masa mota. Shiko Anas ko a kwalar rigarsa daman haka yake so, tana aikinta me kyau ba shisshigi. Washegari ya kasance Asabar ba aiki Anas kuwa through the week yasaba da karyawa da coffeen Fannah sam yak’i cin breakfast seya sha coffeen ta tukunah. Wayarsa ya d’au ya kirata da misalin k’arfe 10:30AM alokacin se shiri suke ita da Afrah zasu gidan wata k’awar Afrah data haihu tun bata gama secondary school ba aka mata aure, zasu yin barka. Fannah tayi bala’in kyau tunda nake ban tab’a ganin Fannah tayi kyau kamar na yau ba dake Afrah ce ‘yar gayu ta mata kwalya. Brick red jan baki tasa mata da kwalli da lining sannan ta taje mata dogayen gashin idanunta da mascara ta mata brushing gira tare da shafa mata powder had’adden daya mugun amsar skin nata. Sanye take da blue and red atamfa amman red d’in yafi yawa dan dolenta tasa gyale sabida Afrah ta tak’ura mata. Tana zaune tana game tana jiran Afrah wayarta ya soma ringing ganin Mr. Fauzi ke kira ya mugun bata mamaki yaude Asabar ce bakuma ranar aiki ba toh me zekira yace min? Ta tambayi kanta a zuci. “Afrah kiga Mr. Fauzi ke kira meze cemin?” “Taya zamu sani in bawai d’aga wa kikayi ba Ya Fannah.” A hankali ta d’aga tasa a kunne. *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:48, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 2⃣5⃣ “Hello” tace a hankali. “coffee nakeso.” Ya fad’a authoritatively. “Sir amman ai yau saturday ne ba’a aiki a weekends.” “In Boss naki yace se kinyi kuma fah? Can you say no.” Can k’asa k’asa tace, “a’a.” “Good, meet me at my paint house...” Nan yamata kwatance kafin tace, “okay” ya katse wayar. “Meh yace wai?” cewar Afrah dake d’aura kai. “Wai coffee yakeson sha inje in samesa a paint house nasa.” “Ranan Asabar d’inma?” “Humm! sekace bakisan Mr. Fauzi ba? Haka yake d’an ra’ayi ne.” “Kina nufin yanzu bara muje gidan Haleeman ba kenan?” “Zamuje mana ai had’a coffee kawai zan masa within 2-3 minutes nagama semu tafi yanzu kiyi ki gama shirinki muje tare.” Da “toh” Afrah ta juya ta gama d’aurin ta sannan sukayi sallama da Mami daidai gaban paint house na Anas kamar yadda ya mata kwatance suka tsaya bayan ta sallame me napep d’in suka tsaya admiring gidan dududu barefi 2 bedroom flat bane ciki fari ne tas gidan ya k’ure kalman kyau. “Ya Fannah wannan ne motarsa?” Tana nuni da yatsa. “Wai ba” cewar Fannah. “Wow! Wow!” “Ke kin fara ko? Nikam kizo mushiga” “Wa? ni? In shiga? Saboda ya koreni kimin dariya? Kefa kikace baida mutunci a dalilin me zan biki ciki? Nide kiyi sauri ina jiranki nan.” “Amman Afrah bakiyi ba wallahi ai da sekice min baraki shiga ba, da bamu sallami me napep d’inba.” “Oho sorry zamu samu karki damu, kiyi sauri kar muyi latti.” “Afrah da Allah mu shiga wallahi bansan shiga ni kad’ai.” “Ya Fannah dan Allah kibar had’a ni da Allah dan wallahi barin shiga ba. Off you go” ta mata gwalo. Baki Fannah ta murgud’a mata sannan tayi hanyanta ciki. Door bell data gani bakin k’ofar ta danna zuciyarta se bugawa yake tana jiransa. Bayan kamar minti d’aya k’ofar ya bud’u. Anas tagani tsaye jikin k’ofar ko singlet babu jikinsa bale kaya ¾ wando ne na soja jikinsa, da alama yanzu yafito daga wanka danko gashin kansa a jik’e yake kad’an kad’an ruwa na d’iga a k’asa, ga wani kyan da skin nasa yayi a jik’e har shining shining yake. Blue eyes nasa kuwa sun sake shiga ba k’arya yayi kyau sosai ga body kam masha Allah very muscular ta kasa dena kallonsa kamar yadda shima yake kallonta and for the first time bada wata manufa ba. Be tab’a ganinta da shiri irin na yau ba, kullum cikin hijabi take banda gyalen data yafa yau ga d’an kwaliyan datayi wanda be tab’a gani tayi ba. Sosai ta canza kamanni, ga yadda Afrah ta yafa mata gyalen, ta d’an bar kad’an daga cikin k’irjinta dake a cike dadai ‘yar budurwa a waje. Za’a iya ce miki kinyi kyau ya fad’a a zuciyarsa. Kusan a tare suka kawar da ido daga kan junansu gyalen dake wuyanta ta d’aga ta yafa kai tare da rufe k’irjinta dashi. Kad’an ya matsa gefe “come in” yace da ita a hankali ta shiga ta tsaya ba daga nesa ba “ga chan kitchen d’in” ya nuna mata da yatsa k’ok’ari tayi kar ta sake kallonsa kafin ya silleta. Kai ta giad’a nan take ta tuna dokokinsa tace, “okay.” A sanyaye tabi direction daya nuna mata ta shiga kitchen d’in komai tsatsaf ba datti ba wari. A gefe guda ta hango coffee machine gefe guda kuwa fridge. Wajen fridge d’in ta nufa ta bud’e as expected taga bottles na giya jere daban daban kai kawai ta kad’a taciro abinda zata buk’ata ta nufa wajen coffee machine d’in ta ajiye cupboards d’in tabi tana bud’ewa har tasamu na cups and spoons. Sosai ta mayar da hankalinta gu d’aya gudun kar ta fasa masa d’aya daga cikin fancy cups nasa yasata biya. Bayan ta gama had’a masa ta d’auka da hannu bibbiyu shes very careful ta bud’e k’ofar a hankali ta rufe tana juyawa kawai taga mutum tsaye gabanta gashi har yanzu besa kaya ba ¾ wandon ne. Tsorata tayi sosai iya tsoro dayasa tayi b’arin coffeen saura suka zube a jikin Anas dako singlet baida saura kuma jikinta saura a k’asa. Da cup da plate data d’aura kai dakuma spoon d’in duka suka fashe a k’asa. K’ara sosai Anas yasaki dan zafin coffeen ita bata ma damu da kanta ba, batasan ma yatayi taciro gyalenta ta soma goge masa jikinsa ta cikinsa dashi ba “sorry sir, I’m so sorry dan Allah kayi hak’uri” duk ta rikice. Kallon ta ya tsaya yi cike da mamaki tab’a masa jiki ma take, lallai kuwa. Alokaci d’aya kuma ta tsaya cak! A kunyace ta d’aga hannunta daga jikinsa ta d’aga kai suna had’a ido tayi sauri ta kawar da kanta. “I’m sorry” tace kallonta ya tsaya yi, besan meke damunsa ba, shi d’inda ko matan turawa kan bikini (pant and bra) ma basu masa ba mesa yake kallon Fannah toh? Me take dashi? Jik’ak’en mayafinta ta bud’e zata yafa ya kama karap! A razane ta d’ago kanta tana kallonsa alokaci d’aya tana k’ok’arin fisgan gyalen sede k’arfinsu ba d’aya bane. Ganin ba mahalicci se Allah kawai ta d’aura hannayenta biyu tana tare k’irjinta da kanta k’asa har yanzu Anas be motsa ba kallonta yake sosai sosai da ta d’aga kai seta ga ita yake kallo. Da k’yar tayi gathering courage ta bud’e baki zatace masa “kabani mayafina” kawai ya juya ya fice da gyalen zuwa wata d’aki. B’ari sosai Fannah take, shikenan tabar Anas yaga jikinta duk laifin Afrah ne da hijabinta ne da asirin ta a rufe. Ido ta d’aga sama “Ya Allah ka yafemin astaghfirullah astaghfirullah.” Daidai lokacin Anas ya fito daga d’akin da wani leather a hannunsa baya ta juya take tana kare k’irjinta seda yagama matsowa kusa da ita ta tuna kayan tan ma show me your back ne sanda tace wa d’an iskan tellan su kar ya mata yak’i ji. Kallon spotless bayan ta yake da gashi kad’an kad’an kwance luf akai uban gashinta kuwa an kama sa a tsakiyar kanta wanda dan uban yawansa still sanda yafito daga d’an kwalinta. Sanda ya k’are mata kallo tukuna ya bud’o leather’n har yanzu Fannah bata juya ta kallesa ba ita alhamdulillah tunda be tab’a ta ba. Ta gommaci ya kalli bayanta dayaga k’irjinta. Zuciyar ta kuwa se bugun d’ari d’ari yake. K’aran leather tajiyo a lokacin dayake ciro gyalen daga cikin leather’nsa wani tsoro tasakeji ya ratsa ta se addu’o’i take ta suburbud’owa idanta gagam ta rufe. A hankali taji sauk’an gyale ajikinta a razane ta juya tagansa tsaye a bayanta kwata kwata distance dake tsakaninsu befi inchi uku ko hud’u bane. Da sauri ta rufe jikinta dashi dukda kuwa gyalen shara shara ne amman yafi babu, gashi kuwa yayi kalan me tsada sosai gashi kuma sabo gal. Stepping back tayi “nagode” tace tanasan tambayansa ina gyalenta sekuma ta fasa. Tsugunawa tayi zata tattara broken glasses d’in ya cafko ta da hannu “so kike ki sake yankewa kimin kuka anan? Ko an fad’a miki inasan tab’a jikin ki ne?” Wai ace mutum yanzu ya gama showing kindness wa mutum kuma yana zaginsa, wani hali sena Anas. Fannah tayi tunani a ranta. Hannunta take k’ok’arin fisga dan zafin rik’onsa amman ta kasa, yana noticing haka ya sake ta. “Wuce ki sake had’a min wani coffeen akoi flask akan counter d’in ki cika min shi in kin gama ga kud’inki” ya nuna mata bundle ma N100 kan dining table. Fat zuciyar Fannah ya buga bade korarta daga aiki zeyi ba saboda ta fasa masa cup. “Mr. Fauzi I’m sorry dan Allah don’t fire me ba da gangan na fasa maka cup d’inba ka fad’a min nawane kud’in I will pay you but kar ka koreni please.” Ita ba komi ke damunta ba inbanda kud’in magunan Baba gashi sun kusa k’arewa. Kallonta yake wani eri “and waya gaya miki kinada kud’in da zaki iya biya na kud’in cup d’innan. Humm!” Ya d’an yi murmushin rainin hankali. “Incase clueless mind naki na ce miki firing naki zanyi to ki kwantar da hankalinki wannan kud’in saki aiki ranan saturday ne becareful karki fasa min wani cup d’in saboda zan iya saki biya ko inyi pressing charges.” “Nagode” tace masa tana kallon farin cikinsa dayayi turning ja saboda zafin k’onuwan amman ko kad’an Anas bai nuna yaji zafin k’onar ba. Duk laifinta ne yanzu ta k’ona masa ciki. “Kibar kallo min jiki haka.” Haushi da kunya taji duk lokaci d’aya ita bawai kallonsa take saboda he is hot ba tausaya masa take dan ta k’onasa. “Sir ni bawai kallonka nake saboda inajin dad’in hakan ba, I’m concerned saboda ni na k’ona ka, ka shafa vaseline awajen dan hanasa tashi.” “Kuma se akace miki kina da right na tausaya min kokuma na fad’amin abinda zanyi? Jiki na ne ba naki ba, kawoki gidan nan nayi ki had’a min coffee bawai kizo kina kallo na kina fad’amin abinda zanyi ba, banasan shisshigi.” Mamaki ne yacika Fannah shi da ya tsaya yana kallon k’irjinta da bayan ta d’azu batayi magana ba se shi. Ji take kamar ta sissile sa amman tsoro takeji kar ya koreta. “Allah baka hak’uri” tace kanta a k’asa tare da juyawa kafin ya sake cakka mata wata bak’ar maganar. Bayan minti shida tafito daga kitchen d’in tare da tsallaka fasassun glasses d’in ta ajiye flask d’in kan dining sannan ta koma ta d’au cup d’in taje ta ajiye masa kan side tables na kusa dashi a parlour. Ko kallonta beyi ba wani magani ne a hannunsa yana shafawa kan inda ta k’onasa. Ba tare da tace masa komi ba ta wuce ta d’au jakarta tare da sa kud’in daya bata cikin jakarta tazo fita kenan ya tsaida ta. “Wajen kuma ni zan share?” Baki na rawa tace, “a’a.. A’a” komawa tayi ta ajiye jakarta “ina tsintsiya da moper’n suke?” “Nima bansani ba” ya bata amsa “just go zan kira masu giara su share kafin ki sake min wata b’arnan tunda you are too clumsy” Danne zuciyarta tayi “Nogode” tace masa sannan ta fice. Afrah har ta gaji da jiran Fannah ba sak’e sak’en da batai ba a zuciyarta. “Ya Fannah ya kika jima haka? I thought kince minti hud’u ma yayi yawa.” “Da wannan mutumin?” Ta nuna gidan Anas da yatsa. “Ai aikin minti uku seya sa mutum yayi minti ishrin.” “To mayafin ki fa?” Cewar Afrah “Ina yake waya baki wannan?” “Ke dogon zance muje gidan Haleemar tukunnah zan miki bayanin komai bayan mun isa gida.” Wani kallon tsiya Afrah ta soma mata wanda tuni ta tand’e k’eyarta sanda ta tsaya ta giara d’aurin sannan suka fice. *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:48, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 2⃣6⃣ Bayan Anas ya gama shafa maganin kan ciwonsa ya kurb’e coffeen sa hankali kwance. Yana gamawa yasa kaya yaja motarsa zuwa gida. Amal na tsaye bakin k’ofa tana jiransa. Ko gama fitowa daga mota beyi ba tayi kansa tana masa oyoyo a garin haka tad’an fama masa k’onuwansa. K’ara yasaki kad’an. “Ya Anas kaji ciwo ne?” Murmushi ya mata “a’a angel ba ciwo bane.” “Toh Ya Anas kayi ihu fa, mugani.” Tana k’ok’arin d’aga mai T-shirt. Hannunta ya rik’e “don’t worry angel ba ciwo bane.” “Toh Ya Anas ina mayafina daka ce ka siya min zaka taho min dashi.” Nan ya tuna mayafin nata ya bawa Fannah. “Ya Anas kayi shiru ko dama wasa kake baka saya min ba.” “Angel na saya miki mana, naga bashida kyau ne shine na kyautar ma wata mata akan layi but don’t worry zan k’ara saya miki wani kinji?” Kai ta giad’a a hankali tana turo baki. Ganin haka yace da ita, “dauk’o mayafin ki muje mu siyo miki wani yanzu, infact shopping ma zan kaiki ki saya duk abinda kikeso.” “Yeyy! Ya Anas!” dagudu ta shiga ciki ta d’auko mayafinta suka fice. **** Afrah kuwa ta k’osa Fannah tabata labarin abinda ya faru cikin tsakaninta da Anas d’azu, tun a hanya take ta damun Fannah sanda suka iso gida Fannah ta labarce mata komi. Ido wuru-wuru Afrah ta zaro. “Ya Fannah wallahi Mr. Fauzi na sanki irin wanga kallo haka?” “Kefa akuya ce” cewar Fannah “Mr. fauzin yasoni? Impossible tense kenan! bakiga uban rashin mutuncin dayake suburbud’a min bane wallahi.” “Ke baraki gane irin san bane-” Katse ta Fannah tayi “ni banasan ji sekace baki san banida martaba ba aiko da ace ma sonan yake bare aureni ba muddin yaji labarina kamar yadda nima baran auri masifaffen mutum kamar Mr. Fauzi ba. Kinga tashi ki rakani muje mu siyo wa Baba magunansa tunda mun samu kud’i.” “Amman Ya Fannah a gani na ba sekin bar aiki da Mr. Fauzi ba.” “Kamar ya Afrah? Ke bakisan Mr. Fauzi bane wai? Ai barin aiki dashi consider it done monday monday’n nan zan fara nema in Allah ya taimakeni nasamu ai na huta.” “Tunda haka kikace, Allah sa hakan yafi alkhairi.” “Ameen” Fannah tace sannan suka je suka siyo wa Baba magunansa. Wahsegari ma haka ya kirata kan taje ta had’a masa coffee a paint house nasa tun 8:00AM ya kirata amman se kusan to 9:00AM ta isa saboda ta raka Mami kai Baba ganin likita daga can ta biya gidan Anas tare da mayafin daya bata, ta wanke sa harda guga. Hijabi har k’asa take sanye dashi yau. Bayan ta danna door bell ta tsaya jira shiru dan haka ta sake dannawa nan ma shiru, yin haka sau uku taga ba motsin mutum gidan ta d’au wayarta ta kirasa alokacin da ya soma ringing kuwa wayan na hannun Amal tana game. “Ya Anas coffee maker na kiranka” kafin yace, “mik’a min” ta d’aga “hello coffee maker.” Ido wuru wuru Fannah ta zaro wato ma da coffee maker yayi saving lambarta, Allah shirya toh. “Hello Amal” Fannah ta gaisheta. “Laaa kinsan suna na taya ya?” “Bani wayar Amal” cewar Anas. “Ya Anas gashi ta kira suna na wacece ita?” Nan ta dawo kan wayar “Hello coffee maker ya sunanki?” “Fannah ce Amal.” “Laaaa! Fannah!!” ta daka ihu “ya kike?” “Lafiya, kefah?” “Amal kawo wayan nan.” Nan ya mik’e da nufin ze karb’a ganin haka ta mik’e a guje kafin tace me ya kamata ya k’wace wayan. “Yes? Kud’inki ne baki gani ba komeh?” “Mr. Fauzi gidan a rufe ne.” “Kin gwada bud’e k’ofar ne kika ga a rufe?” Nan tasa hannu taga a bud’e a kunyace tace, “a’a.” “Good kud’inki na kan dining table don’t call me again.” Kafin tayi magana ya katse wayar. Kallon wayar ta tsaya yi lallai ma wannan Mr. Fauzi wallahi da girman kai na kisa da ka juma da mutuwa. Tsuka taja sannan ta shiga ciki... **** “Ya Anas shine kace min bakasan wace Fannah ba ranan dana tambayeka.” Kallon Amal ya tsaya yi yana tunanin wani k’arya ze mata can yace, “eh mana ban santaba, ni banma san asalin sunan ta ba se yanzu, bakiga da coffee maker nayi saving number’nta ba.” “Toh Ya Anas mesa ta kiraka?” “Aiki zatamin.” Ya amsa ta a takaice. “Toh Ya Anas bani lambarta inasan muna waya da ita.” “A’a Amal, Fannah is not a good person bana san kuna zumunci da ita.” “Mesa Ya Anas?” “Just trust me kinji Angel?” “Okay Ya Anas” ta masa murmushi “bani wayar in cigaba da game d’in toh.” Ba gardama ya mik’a mata “zan d’an fita in kin gama ki had’amin a charging kinji?” Kai ta giad'a “and also karkiyi recieving min calls, Angel am serious.” “Ya Anas barin yi ba seka dawo.” “Yawwa Angel!” Be zarce ko inaba se paint house nasa alokacin kuwa Fannah har ta gama had’a masa cikin flask ta ajiye kan dining ta tafi. Dad’i yaji dan ba san ganinta dama yake ba sesa ma yace tazo time da bayya nan. Tun jiya daya ganta ba mayafi ya riga tunaninta wanda ya mugun basa haushi. Nutsuwa yayi ya sha coffeen sa sannan ya taho da flask d’in da ze dawo gida. **** Fannah na zaune ita kad’ai a d’aki tun dawowarta take zaune shiru kasancewar Afrah ma ta tafi yawonta, su Mami kuwa basu dawo ba. Dadai zata d’au wayarta dan buga game kenan wayar ta soma ringing ganin sabuwar lamba ta tsaya nazarin kowaye amman sam bata san lambar ba sanda ta kusan tsinkewa ta d’aga nan ma batace komi ba, familiar voice taji “Fannah” aka kira sunanta. “Na’am Amal ce?” “Kin gane ni kenan?” “Eh!” Fannah ta fad'i cike da mamaki. “Ina kika samu number na?” “A wayan Ya Anas karki fad’a masa munyi waya fa kinji? Besan na d’auka number’nki ba.” “Toh Amal barin fad’a masa ba. Mesa kika kirani?” “Kawai I want you to be my friend.” Cike da mamaki Fannah tace, “toh nikuma? Ai na miki babba.” “To ki zama big sis d’ina” Amal ta fad’i tana turo baki. “To Ya Anas fa bare miki magana ba?” “Ai bare ma sani ba dan ni ba fad’a mai zan ba, kamar yadda kema baraki fad’a masa ba koh?” “Sosai” Fannah tace tana dariya “toh little sis barin fad’a masa ba.” Hira sosai suka sha suka riga tambayan juna questions akan rayuwarsu suna amsawa se can sukayi sallama. Washegari... Kasancewar yau Monday Fannah ta tashi tayi shirin zuwa office tare ta taro credentials nata dan daga can tana san ta wuce neman aiki. Takwas da ‘yan mintuna aka ta isa office bayan tayi knocking Anas yace, “come in.” Kanta sunkuye tashiga ta gaishesa be amsa ba bale ya kalleta, matsowa kusa da shi tayi alokacin ne ya d’ago kai yana kallonta. Jakarta ta bud’e taciro gyalen daya bata kafin ta ajiye kan table d’in ya dakatar da ita. “Wannan kuma fa? Kar ki ajiye min kan table” Ya tambayeta. Cak! Ta dakata “Sir mayafin daka bani shekran,jiya ne thank you, shine zanyi returning maka yanzu.” “Inada ido ai, banaso, bana buk’ata. Ko ki cigaba da ajiyewa wajenki ko kuma ki jefar ya rage miki. Make me coffee.” Mamaki ne yacikata bata ce masa komi ba ta mayar cikin jakarta sannan ta ajiye ta wuce ta had’a masa coffee bayan ta ajiye ta kallesa “Sir excuse me zan d’an fita but in shaa Allah zan dawo kafin azahar.” Yana sipping coffeen sa tare da duban wasu files “wannan kuma keya dama, iyaka in bakizo on time bane inyi firing naki” ya fad’a mata ba tare da ko ya kalleta ba. A ranta tace ka kwantar da hankalinka ina samun aiki zanyi resiging a nan. Jakarta ta ja ta fice neman aiki ta tayi amman ba sa'a kafin azahar ta dawo ta sake had’a masa coffee. Haka de tun daga ranan Fannah ta shiga neman aiki ba wasa. Mayafin kuwa ta adana sa gu d’aya dukda bata da niyyar sake sawa. Anas kuwa be canza ba baya shiga harkanta amman ko d’an k’aramin mistake tayi ze balbaleta ya tsawa ta mata, kuka take sosai duk sanda ya masifeta sam takasa sabuwa da masifar Anas, shiko kukanta sam be d’aga sa bale ya nana sa a k’asa. Shak’uwa sosai yashiga tsakanin Fannah da Amal wanda har yau Anas be sani ba. A yau wata d’aya da sati biyu kenan tana masa aiki. Yau ranar ta kasance Wednesday, dawowar Fannah daga aiki kenan idanunta duk sunyi ja saboda kuka. “Fannah ya haka?” Mami dake fitowa daga kitchen ta tambayeta. Kare fuskarta take “ba komai Mami dutse ne yashiga min ido amman yafita karki damu.” tamata k’arya. “Are you sure?” “Eh Mami ina Aiman da Afrah?” “Sun shiga nan mak’ota.” “Okay barin watsa ruwa toh” nan tayi hanyan d’akinsu. Bayan tafito daga wanka tajiyo alert a wayarta tana dubawa taga message daga d’aya daga cikin ma’aikatan datayi applying FCB ltd. Tsalle ta daka ganin aiki suka bata kuma akan abinda ta karanta finally zata samu tayi amfani da ilimin data samu a jami’a. Afrah na dawowa ta labarta mata komi sosai Afrah ta mata murna. Ga albashi me kyau daidai N50,000. Bayan ta sa kaya taje tayi printing resignation letter’n da zata kaiwa Anas gobe. A hanyar dawowarta gida Amal ta kirata bayan sun gaisa take fad’a mata kan tabar aiki a Enterprise na Anas tasamu aiki. Amal ta mata murna kam sede bataji dad’in barin aikin Fannah gun Anas ba. Sau dayawa tana zuwa office na Anas ita da Fannah su fita suje suta hira ba tare da sanin shi Anas d’inba. “Ya Fannah amman mesa zaki bar aiki da Ya Anas? Ya miki wani abu ne?” Murmushi Fannah tayi sam halin Anas da Amal ba iri d’aya bane, kamanninsu ne kawai d’aya. “Ba abinda yamin Amal kawai nasamu better job ne.” “Yanzu shikenan bara mu sake had’uwa ba?” ta fad’a kamar zatayi kuka. “Nima banso hakan ba Amal, amman ai zamu na waya ko?” “Eh amman its still not enough ko zaki na zuwa gidanmu?” Danqaree Fannah tafe a zuci. “A’a Amal bareyi inje gidanku ba saboda Ya Anas.” “Ba abinda Ya Anas ze miki dan Allah kinji?” K’arya ta mata “naji zanzo in shaa Allah. Ina kan hanya bari in na isa gida zan kiraki.” A haka sukayi sallama. Washegari Fannah tasha baccinta a cewarta ta bar masa aiki se lokacin data ga daman zuwa office zata takai masa resignation letter’nta. Da misalin k’arfe 9:30AM Fannah ta iso building na Anas. A first floor ta had’u da Yusuf ta sanardashi great news na aikin data samu sosai yaji mata dad’i kuma ya mata murna. “Barin haura inkai wa Mr. Fauzi resignation letter na ina zuwa.” Da “toh” ta shige elevator. Zuciyarta fal da farin ciki ba me sake sata kuka yanzu dan ta tabbata ba worse Boss kamar Anas. Knocking d’aya tayi a bakin k’ofar yace, “come.” Cike yake da ita wato yau se 9:34AM Fannah taga daman zuwa masa office, she will get it from him. Bayan ta k’ariso ciki ta gaishe sa ko amsa ta beyi ba kallo ya watsa mata wanda yasa k’afafunta shaking. Ya bud’e baki ze soma suburbud’o mata masifa kamar an turosa kawai k’ofar office d’in ya bud’u wanda ba kowa ke shigowa haka ba illa Amal. “Ya Fannah!” tayi ihu ganin Fannah tsaye da gudu ta nufa wajenta tayi hugging nata. Baki wangalau Anas ya bud’e yana kallonsu. Wato Amal bata je school ba yau, bama wannan ba yaushe suka san juna da Fannah har suka shak’u haka? Tambayoyin da yayi wa kansa kenan. “Ya Fannah yanzu dagaske kike zaki bar aiki nan? Dan Allah kiyi hak’uri.” Kunnensa ya bubbuga ko halan ruwa ya shiga yau da yake wanka, barin aiki Fannah zatayi zuwa ina? Ta samu wani aiki ne? Coffee na fa? Bece dasu komi ba sanda suka gama hoge-hogensu. Bayan Fannah ta ciro letter’n ta matso kusa da table na Anas. “Mr. Fauzi wannan resignation letter na ne. Thank you for giving me the oppurtunity to work for you.” Letter’n ya d’aga yana k’arisa masa kallo sannan ya d’ago blue eyes nasa yana kallonta “are you really sure about this? Na barin aiki a nan?” ya tambayeta ba tare da ya nuna damuwa ba dukda kuwa ya damu sosai. Kai ta giad’a a hankali. “Kin samu wani aiki ne?” Nanma kai ta kuma giad’awa. “A ina?” “A FCB ltd.” ta amsa sa. “Ohhh, nawa ne salary’n naki?” K’arya tayi masa “nima bansani ba tukunah.” “Yayi kyau zaki iya tafiya.” Amal dake kallonsu ne tace, “Ya Anas ka hana ta tafiya ka k’ara mata salary se kar ta tafi.” “A’a Angle barta ta tafi. Ni ban hanaki alak’a da ita bama?” Ya tambayeta ba alaman wasa a tattare dashi. “Ya Anas kayi hak’uri.” “Zan hak’ura if only kika dena alak’a da ita, kingani ai barin aiki tayi.” “Mr. Fauzi-” cewar Fannah be saurareta ba ya daka mata tsawa “just go, leave, bana san sake ganinki.” “Amal na tafi” nan ta juya. “Ya Anas-” itanma tsawa ya daka mata for the first time. “Enough Angel kije ki samu Yunus yakira Shettima yazo ya d’auke ki.” Ita kanta tsoro taji sosai bata tab’a ganin mood na yayanta haka ba. Wajensa ta nufa tayi hugging nasa “Ya Anas I’m sorry, bansan me Ya Fannah tayi ka tsaneta haka ba, tanada kirki fah but tunda baka sona tare da ita, I’m sorry.” Bayanta ya shafa “is okay je gida ki huta nima I'm sorry for shouting at you.” Bayan Amal ta fice Anas ya d’au resignation letter’n Fannah ya yayyaga into pieces, zuciyansa se tafasa yake. Yarasa me ke damunsa mesa ma nake damuwa dan wata wai ita Fannah tabar min aiki? Nawa suka fi ta komi kuma na koresu, toh se meh dan kin bar min aiki? Mschww dama dan coffee ne kuma akoi masu neman aiki anan dubu. Wayarsa ya d’au ya kira Ahmad. “A buga a news ina neman masu aiki wanda suke da degree inma da hali har da masters kan had’a cofee.” Cike da rashin fahimta Ahmad yace, “Boss coffee kuma? Anayin course akan coffee ne?” A fusace Anas yace, “in baka aiwatar da abinda na saka kayi ba a yau a bakin aikinka.” Tuni Ahmad ya amsa “yes ofcourse Boss” “Good, kuma ka turo cleaners suzo share wannan gabbage” yana nuni da resignation letter’n Fannah daya yayyaga “and also ka turo min number’n manager’n FCB ltd” *Ina me baku hak’uri masu karatu bansamu nayi typing ba yau sosai, gobe in shaa Allah zaku jini* *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:49, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 2⃣8⃣ Da yammacin ranar Juma’a bayan Anas ya dawo daga office yayi firing mutane 6 shida ranan. Kwance yake kan gado a d’akinsa ya zura wa ceiling ido yayi zurfi cikin tunani. Har Shettima yayi sallama ya shigo beyi noticing ba. D’an tab’a sa yayi a hannu firgit ya dawo daga duniyar tunanin daya fad’a. “Ya Anas yaukuma tunanin me kake haka? Na Ummimi kokuma na yarinyan?” ya tambayesa yana k’ok’arin zama kusa dashi. “Ko d’aya” ya amsa sa alokacin dayake k’ok’arin zama. “Then mene? Kasan ban maka magana bane amman Yusuf yabani labarin abinda kake tayi a Enterprise naka, me yayi zafi ace cikin sati kayi firing mutane 31 haba Ya Anas.” “Oh haka shi Yusuf nakan yace? Allah kaimu monday shima ya jira nasa.” “Ya Anas wai me haka, friend nawan zaka kora? Wace kuma Fannah?” Cike da mamaki Anas ya kewayo da blue eyes nasa kan Shettima. “A ina kuma kaji wannan batu? Still gun Yusuf?” “It doesn matter Ya Anas saboda ita kake firing ma’aikatan ka kana kashe Enterprise naka da kanka, ajinka yanzu in za’a dawo da Baba zeyi appreciating abinda kakeyi ne?” “Toh yimin lectures Shettima, please ni banasan maganan nan excuse me.” “Saboda yarinyan ne Ya Anas, kanasan ta dawo maka aiki ne? Do you miss her?” A fusace yace, “Yes Shettima I do, I miss her.” “Toh mesa kake treating nata badly lokacin da take nan? Kaifa kasa tayi resigning tabar maka aiki.” “Shettima ni ba abinda yake damuna ba kenan, abinda yake damuna shine tadawo.” “Toh ta yaya?” “Ta duk yadda nasan zan iya.” Shiru Shettima yayi yana nazarin wani abu. “What are you thinking of?” Anas ya tambayesa. “Ya Anas kode san ta kake? Yaushe ka fara damuwa da rashin mutum a kusa da kai?” “San ta? Are you kidding me Shettima? Me zan so a jikinta? Ni kawai I miss her saboda coffeen da take making min.” Yama Shettima k’arya dan shi kansa yanzu yasan ba coffeen Fannah kad’ai yake missing ba no matter how yayi denying Fannah ta daban ce, kayan duniya be dame ta ba, kyansa dayasa mata suke binsa ma be dameta ba yaci ace Fannah ta kamu da ciwon sansa amman ko kad’an beyi noticing hakan ba a tattare da ita. “Amman da akoi abin duba anan mata nawa wanda suka fi Fannah komai suke fad’in suna sanka baka tab’a saurara musu ba hasali ma koda sun shigo rayuwarka k’ok’arin koransu kake amman when it comes to Fannah, ita ta tafi da kanta but kanasan dawo da ita. Ya Anas ina yarinyan dakace *_TANA TARE DA KAI?_* Ko hala itace Fannan.” “Non sense. Wani erin jagual guale kake fad’i Shettima? That girl can’t be Fannah in da ace itace da nayi recognising nata. Ka manta lokacin da abinda ya faru a buge kake?” “Toh ita fah? Ai in ni a buge nake ita ba’a buge take ba, da itace da ta gane ni.” “Not really” Shettima ya fad’a yana kad’a kai. “Noo Shettima wancan yarinyan ba Fannah bace kadena had’ani da Fannah please ni ba wai santa nake ba, batta,da abinda zan gani har ince inaso duk mata ma ba wacce take dashi illa yarinyar dake *_TARE DA NI._* so please kabar had’ani da Fannah, coffeen ta nakeso ba itaba.” Shettima ze sake magana Anas ya katse sa “maganan Fannan kuma ya isa please. Zan kwanta excuse me” kallonsa kawai Shettima yayi ya kad’a kai sannan ya fice. “Mesa Shettima zece inasan Fannah? Mesa yake tunanin itace yarinyar da nake nema har yau, eh nasani yarinyar *_TANA TARE DA NI_* amman ba itace Fannah ba, banasan Fannah barin tab’a santa ba coffeen ta kawai nakeso. Coffeen ma daga yau zan dena missing saboda in manta da ita a rayuwa na forever” Washegari ya kasance Asabar ko tashi daga kan gado Anas beyi ba ya fara tuna Asabar daya kira Fannah zuwa gidansa had’a masa coffee, k’irjinta daya gani tun ranan har yau yakasa deleting image d’in daga k’wak’walwar sa. Kai ya kad’a dan ya gusar da tunanin nan ya mik’e ya shiga bathroom ya kunna shower yabar ruwan na sauk’a kansa. Duk yadda yayi ya mance Fannah ya kasa, yarasa dalili is not as if yasan how it feels to be in love. _One week 2 days later..._ A shekaran jiya Manager’n FCB ltd ya dawo tun a ranan secretary’n yama Anas sending number’n Boss nasa as promised sede abin mamaki har yau Sunday Anas be kira manager’n ba. Kwance yake a d’akinsa da wayarsa a hannunsa ya zura wa lambar Manager’n ido yakasa kira. Anas ya koma wani abu daban. Sati biyu ne tun rabuwarsa da Fannah amman seji yake kamar irin shekara da shekaru. Abin nasa se worse yake dukda maganar da Shettima yamasa amman ina. A yanzu haka yayi firing about 60 something staffs nasa kullum cikin kawo sabi ake, hankalin kowa ya tashi a office sede ba kamar yadda na Anas ya tashi ba. Mutuwa ne kawai beyi ba dan hana kansa tunanin Fannah da coffeen ta. Yanzu haka ma ga number’n Manager’n amman ya kasa kira dan girman kai. Seda yammacin ranan ya danna wa manager’n kira, he can’t take it anymore. Manager be d’aga ba a karo na farko se ana biyu nan ma sanda ya kusa tsinkewa. “Hello” Manager’n yace bayan ya d’aga. “Mr. Azeez, Anas Fauzi ne.” “Ohh our youngest billonaire! Kwana dayawa.” “Alhamdulillah tun last 2 weeks nake neman ka akacemin ka tafi trip hungary, I had to wait ka dawo.” “Taya Kabeer ze maka haka? Besan ko waye kai bane? Ai be fad’a min ba I’m sorry.” “Ba komai ya wuce dama aiki nakeson baka.” “Toh billonaire inaji...” “About last 2-3 weeks kukayi employing ma’aikata koh?” “Eh suna nan ma munajin dad’in aiki dasu musamman wata Fannah something yarinyan akoi hardwork ina tunanin k’ara mata matsayi ma.” D’an murmushi Anas yayi “ita nakeso kayi firing Mr. Azeez.” Ido wuru wuru ya zaro “inyi firing nata kuma billonaire? Mesa?” “Saboda ni nace.” “Toh nawa kuma zaka bani wannan karan?” Murmushi yasaki kad’an again. “Miliyin d’aya yayi?” Mr. Azeez lips nasa ya tand’e tas “amman barin samu k’ari ba?” saboda yasan irin kud’ad’en da Anas yakeda. “Inde zakayi firing nata zan k’ara maka 1.5 yayi?” “Wow! consider it done Mr. Fauzi saisa nakeson aiki da kai wallahi. Gobe gobe za’ayi kamar yadda kakeso.” “Good” Anas yace yana me jin dad’i “amman kasan be kamata kayi firing nata haka kawai ba zan turo maka 50k akai se ka bata please make sure ka bata, banaso na bata kud’i dayawa tak’i dawowa wajen aiki” “Karka damu Mr. Fauzi zan san yadda zan b’ullo mata da lamarin ta yadda barata fahimci you have something to do with this ba.” “Good nagode.” “Ai ba godiya tsakanin wa da k’ani. Take care” ahaka sukayi sallama. Sosai Anas yaji dad’i dan dolen Fannah ta dawo masa aiki yanzu kuma wannan karan ma better job ze bata yadda bara ta sake tunanin tafiya ba, yasamu yasha coffee iya san ransa. Aiki kamar Personal Assistance nasa tunda dama baida shi. Jira kawai yake gobe ko jibi yayi Fannah ta dawo masa aiki. **** Fannah na zaune d’aki ita da Afrah se hira sukeyi cike da nishad’i. Har wani fresh Fannah ta k’ara dan yadda batta da wani matsala yanzu. Wayarta ce ta soma ruri nan da nan ta duba ganin Yusuf ke kira yasa ta d’aga da wuri. “Assalamu alaikum Yusuf” “Wa’alakissalam Fannah ya kike? Ya aiki?” “Lafiya qalou, aiki alhamdulillah, naka fah?” “Fannah wallahi wajen aiki ya zamo kamar hell.” “Mesa kace haka Yusuf?” Ta tambaya cike da rashin fahimta. “Wallahi Boss ne Fannah, Boss yazama wani abu daban tun tafiyar ki, da barin ki office d’in wallahi yayi firing mutane sittin da abu ka.” “What! Allah shirya!” Fannah tayi exclaming cike da mamaki. “Sittin da abu? Dalili?” “Saboda ke mana Fannah, wallahi Boss yayi missing naki frustration na rasa ki yasa yake duk abinda yakeyi.” “A’a kam bade ni ba, nikuma me had’ina da Mr. Fauzi? Ai Allah ya riga ya rabani dashi har abada in shaa Allah.” “Fannah ki tausaya mana ki dawo please, wallahi kina dawowa komi ze dawo normal.” “Yusuf!” Ta kira sunansa cike da mamaki “nima ka tausaya min mana, ashe de baka sona kafi kowa sanin abinda Mr. Fauzi yakemin ni barin aiki dashi shine mafi alkhairi a gareni kukuma Allah k’ara maku hak’uri amman inde dan in dawo aiki k’ark’ashin wancan mugun mutumin ne ka kirani I’m sorry I can’t.” Karap ta katse wayarta. “Wani mara imanin ne Ya Fannah?” Afrah dake game a wayarta ta tambayeta. “Yusuf ne wai in dawo aiki a Flames Enterprises...” nan de ta labarce mata komi. “Ayya amman sun ban tausayi gaskia shege Mr. Fauzi an gasu!” ta fad'a tana dariya. Dariyan itama Fannah takeyi “ai ya gasu ya k’one Allah ya riga ya rabani dashi har abada!” _Washegary..._ As usual k’arfe takwas dadai ya cika wa Fannah a office kap co workers nata suna santa dan hali irin nata me kyau. Chan around 10:30AM tana zaune tana faxing wasu papers aka danna mata kira daga Manager’s office zuciyarta fal taje sam basu tab’a samin matsala dashi ba tun dawowarsa ita ta d’au ma batun promotion dayace ze mata ne. Bayan ta shiga office nasan ta gaishesa cike da girmamawa kamar yadda ta saba da fara’a ya amsata sannan ya nuna mata kujera ta zauna. “Fannah Aleeyu kamar yadda kika sani kina d’aya daga cikin hard working employees d’ina ko kad’an bansan rasaki amman in yazama dole kinga ba yadda na iya.” Murmushin dake fuskarta ne ya gushe a hankali. “Bangane ba Mr. Azeez.” “Fannah babban matsala na samu da wannan organisation namu wanda yazama dole in rage ma’aikatan da aka d’iba last 3 weeks wanda nakeso da alkhairi kenan wanda kuma ba haka ba, zasu cigaba da aiki nan amman ba albashi. Inasan ki da alkhairi Fannah sesa zan fara sallamar ki and already na riga na samo miki aiki ma me kyan gaske.” “Allah sarki Mr. Azeez ni ko ba albashin ‘yan watanni zan maka aiki karka damu, inasan aiki anan sosai.” “A’a Fannah” I insist please. “Ga wannan” nan yaciro envelope “dubu hamsin ne ciki albashinki na wata gabad’aya.” “Mr. Azeez ai banyi aikin wata ba kayi deducting please seka samu ka biya wasu dashi..” “Ni na baki Fannah ki rik’e karki damu” “Toh nagode sosai Allah saka da alkhairi, matsalar da organisation naka yasamu kuma Allah takaita.” “Ameen” yace yana mata murmushi “Toh Mr. Azeez ina ne inda kace ka sama min aikin?” “Ba ko ina bane se Flames Enterprises.” Take taji zuciyarta ta buga ai ba Flames Enterprises ba sunan chan wajen, hell shi yakamata ana kiran wajen da. “Lafiya Miss Aleeyu?” ya tambayeta. A kid’ime tace, “a’a, a’a nagode Mr. Azeez gobe in shaa Allah zanje nagode.” “You’re welcome, yawwa please karki sanar da wani ko wata maganar da mukayi dake kar su gudu in rasa ma’aikata.” “In shaa Allah na gode da erin karamcin da ka min Allah saka.” Da “Ameen” daya amsata ta fice. Jakarta ta d’auka tama sauran ‘yan uwan nata k’arya kan zata gida. Bayan ta isa gida ta tarar da duka family member’nta banda Aiman dake school zaune suna hira harda Baba dad’i taji sosai Babanta na samun sauk’i. “Fannah ya haka yau?” Tambayar Mami. Murmushi ta musu duka “wallahi matsala aka samu da ma’aikatanmu...” nan de ta zayyana masu komi. Ba wanda yaji dad’i cikinsu saboda sun san wahalar neman aiki. “Karki damu ‘yata zamu taya ki da addu’a in shaa Allahu nan da lokaci kad’an zaki sake samun wani aikin.” Baba ya tabbatar mata yana me mata murmushi. “Gaskiyan Babanku ne Fannah karki damu akoi Allah.” “In shaa Allah Mami gashi kuwa ya biyani albashi na na wata kinga zamu samu mud’an yi siyayya. Afrah zo mu shiga daga ciki.” Shigarsu ciki Fannah tabata labarin aikin da Mr. Kabeer ya nemo mata a Flames Enterprises. K’irji ta dafe tare da zaro ido. “Kin gudu baki tsira ba Ya Fannah ya zakiyi yanzu?” “Nikuwa na gudu na tsira Afrah banga abinda ze sake sani ma Mr. Fauzi aiki ba. Chab! Aiko Mr. Azeez yazo ya kirani nan gaba ce masa kawai zan nasamu wani aikin daban.” Shiru Afrah tayi tana nazarin abu. “Tunanin me kike haka?” Fannah ta tambayeta tare da d’an bugin ta a hannu. “Something smells fishy anan.” Afrah tace tana tunani. “Meh kenan?” Fannah ta tambayeta a takaice. “Mesa Mr. Azeez ze tura ki Flames Enterprises kinsan me nake gani? Gani nake kamar Mr. Fauzi nada hannu cikin wannan abu.” Shiru itama Fannah tayi tana nazarin abinda Afrah tace. Chan ta murmusa “ko kad’an Afrah kin manta Yusuf yace kullum cikin koran ma’aikata yake ai kinga kuwa dole yana neman masu aiki safe da dare and ko ba dan haka bama I trust Mr. Azeez” Kai Afrah ta giad’a nufin ta gane. “Kinyi gaskia kuma fa mude fatan mu Allah baki wani aikin ba sekin wahala.” “Ameen Afrah gobe zan shiga nema in shaa Allah.” ***** Tun k’arfe 9:00AM Fannah tabar gida bayan addu’o’in da su Mami suka ta suburbud’a mata. Mr. Fauzi kuwa yau office nasan ma yak’i shiga yana tsaye bakin k’ofa shi a dole yana jiran isowar Fannah dan tun daren jiya da Mr. Kabeer ya fad’a masa yayi firing nata yakasa hak’ura se Allah Allah yake gobe yayi. Mamaki ne ya cika kowa a building d’in wai yau Mr. Fauzi ke tsaye bakin k’ofa ko wa yake jira se Allah! Ganin har 11:00AM ba alaman Fannah ya dawo ciki da disappointment karara a fuskarsa. Bade ta samu wani aikin ba? In bahaka ba me ze hanata zuwa? Ai sosai Fannah bata wasa da aiki, what could be the problem? Wayarsa ya d’au ya kira Idrees bayan kamar minti biyu Idrees ya iso bayan gaisuwa yace, “yes Boss you called for me.” Giaran murya Anas yayi “aiki nakeson saka and banasan failure, kanajina?” “Inaji Boss fad’a min duk abinda kakeso ayi maka.” *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:49, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 2⃣7⃣ Ko cikakken minti d’aya ba’a yiba Ahmad ya turo masa lambar PA’n Manager’n FCB ltd kasancewar Manager’n ya canza number kuma bayi sabon. Nan Anas ya kira PA’n ringing d’aya biyu PA’n ya d’aga gaisuwa ya fara wanda Anas ya dakatar dashi ransa se tafasa yake dan yadda ya b’aci. “Ka kai wa Boss naka wayan” ya fad’a authorititavely. “Wa ke magana please?” Cewar PA’n saboda bada layin office Anas ya kirasa ba. Ba k’aramin fusatar dashi tambayan PA’n yayi ba. Cike da b’acin rai yace, “Tambaya na ma kake wake magana? Inba wai so kake ka rasa aikinka a yinin yau ba give the damn phone ro your Boss.” Ya sake daka masa tsawa. “Sir I’m sorry but ya kamata insan wake magana kafin in maka abinda kake buk’ata.” “You’re stupid kajini? Nace you are stupid, ANAS IBRAHIM FAUZI ke magana CEO’n FLAMES ENTERPRISES.” “Omg! Sir dan Allah kayi hak’uri wallahi ban san kai bane,my apologies please kayi hak’uri.” Tsuka Anas yaja “mschww damuwanka wannan kuma, where is your boss ka kai masa wayan.” “Sir d’azu da safe Boss d’ina da family’nsa suka tafi trip zuwa Hungary.” “Meaning what? Meaning baraka kirasa kace inasan masa magana ba kenan ko meh?” “Sir I’m so sorry amman sanda ya fad’a min koda wasa kar na kirasa in batun aiki ne dan Allah kayi hak’uri. Hutu ya tafi” “Lalle kanasan rasa aikin ka nace call your Boss kace masa ina san masa magana.” “Mr. Fauzi dan Allah kayi hak’uri wallahi banasan rasa aiki na.” “Damn it!” ya buga hannun sa kan table, “what of business kuna running har yanzu ko shima kun dakatar?” Dadai lokacin knock yashigo daga k’ofar office nasa “come” yace bayan an bud’e k’ofar cleaners mata biyu suka bayyana. Tun daga bakin k’ofa suke gaishesa har suka k’ariso ciki. Papers d’in ya nuna masu nan d’ayan ta hau sharewa kallonsu ya tsaya yi bayan yayi holding call dayakeyi da PA’n. Har sun kai da bakin k’ofa ya kirawo su, dawowa sukayi suka tsaya gabansa “yyyess Sir” har i’ina suke dan tsoro. “Haka ne kin share nan wajen?” Yana nuna wanda ta share wajen “bakiga wancan paper’n bane?” Ya nuna mata wani piece na paper a k’asa. “Me amfaninki a nan in har shara ma baki iya ba se an koya miki? Eh?? Useless kawai.” “Boss dan Allah kayi hak’uri” tana b’ari taje ta share gudan paper’n kallonta yake sannan cike da nuna rashin damuwa yace, “you are fired ki tattara kanki kibar min building kije kisamu Adam yayi settling miki salary’nki. You are dismissed.” Kuka ta fashe da “Boss dan Allah kayi hak’uri wallahi ban gani bane hakan bare sake faruwa ba.” D’ayan ce tasa baki dan ganin yadda ‘yar uwarta ke kuka. “Boss dan Allah kamata hak’uri bada-” Mugun kallo kawai ya mata wanda yasa take tayi shiru. “Kekuma waya jefa bakinki cikin wannan matter? Nasan kinada dogon baki ba sekin nuna min ba I have eyes to see. You two dukan biyu are fired, kuje kusamu Adam yayi settling muku albashinku now leave my office.” Suna kuka suna had’asa da Allah amman ko a kwalan rigarsa tashin hankalin Fannah tabar masa aiki bame had’asa masa coffee ke damunsa nan ya dawo kan wayar. “Nace kun rufe business naku ne ko kuna running har yanzu?” Ya tambayi PA’n. “Muna running Sir komi munayi.” “Good” Anas yace, “kwanan nan kukayi hiring ma’aikata koh?” “Eh Sir just jiya muka musu sending letter ran monday zasu soma aiki.” “Ka bud’e kunnuwanka da kyau kajini. Inasan kaje kabi list d’in kayi firing FANNAH ALEEYU. kajini?” “Naji Sir yanzu zanje in samu secretary in masa magana in shaa Allah za’ayi firing natan. Amman mesa Sir?” “Wannan kuma ba damuwanka bane, inajiran feedback nanda like 10ninutes” “Okay Sir” nan Anas ya katse wayar. Bakinsa ya cize yana murmushin mugunta. Telephone na office nasa ne yasoma ringing nan ya d’aga. “Hello Boss an buga a press da jaridu gobe in shaa Allahu masu degree da masters harda PHD ma zasu soma applying batun coffeen” “Good banasan failure.” “In shaa Allah Boss.” Shide Ahmad mamaki yake har yanzu wai yaushe aka soma yin degree kan had’a banzan shayin da ake had’awa kan tebur akan layi safe rana dare, wani abu se Boss. Kai ya jingina jikin kujerar sa yana juyawa a hankali chan ya mik’e ya bud’e fridge tare da ciro barasar sa kusan rabi ya kurb’e ya koma d’aki ya baje ya kwanta ko problem nasa ze d’an tafi. Sanda ya kusan kai minti goma sannan yasamu yayi bacci abinda kullum daya sha befi minti uku bacci ya rufesa. Bacci me nauyi ne ya rufesa wayarsa dake kan table se ringing yake PA’n Manager’n FCB ltd ke kira. Two missed calls yamasa sannan ya hak’ura. Bayan minti ishirin da kwanciyar Anas, Kacallah ya taho yana knocking bakin k’ofa se sauri yake kwata kwata ya manta Anas nada board meeting da zeyi attending yau saboda yadda aiki ya masa yawa gashi in less than 10 minutes za’a fara. Knocking yake sosai Anas dake bacci ko kad’an baiji daga k’arshe shiga kawai yayi yana kiransa da “Boss” shiru kukeji. D’akin ya lek’a yaga Anas yayi ruf da ciki se bacci yake sha harda minshari necktie nasa yayi gefe guda takalmansa ma d’aya na kudu da’aya kuwa arewa. Ido ya zaro wuru wuru mekuma yasami Boss nasa yake bacci in the middle of the day. K’arisawa cikin d’akin yayi shi kansa tsoron tada Anas yake gudun kar ya rasa aikinsa dan kuwa yaga Hussaina da Zainab da akayi firing d’azu se kuka suke. A hankali ya tsuguna gaban fuskar Anas. “Boss!” ya fad’i murya na b’ari. “Boss!” Nan ma shiru dan haka yad’an jijjik’a sa ko kad’an Anas be motsa ba se bacci yakeyi. “Boss!” Kacallah ya kira sa sosai cikin kunnen sa nan ya yamutsa fuska. “Boss kayi hak’uri ka tashi akoi board meeting da za’ayi wanda yazama dole kaje you are needed please.” Cikin bacci yace, “dole? Se a sani inga. Barin je ba leave ko baka ga bacci nakeyi ba?” Pillow yaja ya rufe fuskarsa. Fuskar Kacallah kan wanda zeyi kuka “Boss kayi hak’uri ka tashi please you have to be there.” “Wake magana?” Anas ya tambayi Kacallah fuskarsa rufe da pillow dan yama kasa recognising muryar meshi. “Kacallah ne Boss, Kacallah ne.” “Kacallah kanason aikinka?” Anas ya tambayesa fuskarsa cikin pillown har yanzu. “Eh Boss inason aiki na sosai” ya fad’i yana giad’a kai. “To ka tashi kabani waje, fita min daga office in na sake jin muryaraka you’ll be fired.” “Fired?” Kacallah ya nanata a zuciyarsa. Meyayi zafi harda firing. Da sauri ya tashi ya bar d’akin hak’urin da yakeson badan ma yafasa dan ko Anas yace baisan sake jin muryar sa. Bayan ya isa office nasu na ma’aikata ya zauna kan table nasa tunanin wani k’arya ze had’ama wanda zasui meeting d’in yake chan ya d’au telephone ya kira assistant coordinator’n meeting d’in bayan ya gaishesa ya fara kamar haka; “Uhm Sir dan Allah kayi hak’uri for the inconvenience da aka samu.” “Wani incovinience kenan?” Mutumin ya tambaya. “Boss d’ina ne mahaifiyarsa ba tada lafiya, bareyi yasamu attending meeting d’inba, kuyi hak’uri please.” “Toh Allah sawak’e amman gaskia bareyi ace Flames Enterprises basu hallaci wannan meeting ba saboda na board ne gabaki d’aya, ka turo d’aya daga cikin staffs naku ya ko ta wakilce sa.” “Yes Sir thank you so much.” Nan ya katse ya kira wata ma’aikaciya Suwaiba dake 6th floor yamata bayanin komi take ta shirya ta tafi zuwa meeting d’in. Nanne Kacallah yad’an samu peace of mind se addu’a yake Allah sa kar emergency ya taso dan besan ya zeyi ba Boss yace bayasan sake jin muryarsa. Bacci sosai Anas yasha kusan to 2:00PM ya tashi da k’yar yayi alwala yayi sallah yayi ordering kawo masa abinci daga kitchen, a lokacin ya duba wayarsa yaga missed calls from PA. Nan ya kirasa, “hello Sir good afternoon.” Ba takan gaisuwar yake ba dan haka ko amsa sa beyi ba, “yes anyi firing natan?” “Unfortunately Sir wallahi secretary’n yace ba abinda tayi wai bareyi firing nata ba-” “What!??” Anas ya daka tsawa. “Bareyi firing nata ba? Waye shi?” Daidai lokacin knock yazo daga k’ofa ransa b’ace yace, “who is it?” Tana b’ari tace, “Boss Leemcy ce abincin ka na kawo” “Banaso, get the hell out of my office you are fired kije ki samu Adam.” Aguje ta koma k’asa tana kuka. “Kace meh? Bareyi firing nata ba? Kai masa wayan.” Bayan minti d’aya aka kaiwa secretary wayar. “Hello yace.” “Hellon k’aniya?” Anas ya tambayesa “kasan dawa kake magana?” “A’a seka fad’a” cewar secretary’n. “Nonsense you are speaking with ANAS IBRAHIM FAUZI.” “Sir! Ran ka ya dad’e kayi hak’uri dan Allah wallahi Kabir be sanar dani wane kai ba.” “Yanzu daka sani seka yi abinda ya kamata” amsar da Anas ya basa kenan. “Yes ofcourse Sir yanzu zan tura mata message d’in.” “Good, inajiran feedback nanda 5minutes.” Karap yayi hanging call d’in. Nan da nan yasa akayi typing message na Fannah daidai lokacin za’a tura Manager’n wajen ya turo sak’o kan kar a d’iba kuma kar a sakar da masu aiki saboda wasu k’wararrun dalilu. Aiko ba halin korar Fannah. Nan ya kira Anas ya masa bayani. “What rubbish are you saying? Ku had’ani da manager’n naku.” “Sir wallahi kayi hak’uri nan da sati biyu ze dawo in ya dawo everything will go your way, sosai Boss yana mutunta ka duk abinda kakeso shi zai maka, ka k’ara hak’uri please ni da kaina zan sanar dakai duk sanda yayi landing.” Dan haushi bema amsa sa ba ya katse wayar. Zuciyarsa tafasa yake kamar ze k’one “mstchwww.” Ma akan Fannah da bata kai ta kawo ba yana ta tada hankalinsa inde coffee ne ai yasa job on sale daga gobe za’a fara applying, se meh dan Fannah tabar masa aiki, aikin banza. Tun lokacin tashi beyi ba ya tattara wayoyinsa ya sauk’a. Chan ma by mistake wata ma’aikaciya tasha gabansa saboda saurin da take tayi submitting wasu files take aka buga mata fire! Itama. A ranan Anas yayi firing mutane ba adadi kowa mamaki yake at thesame time being cautious kuma shima kar a koresa. Kacallah de ba halin yima Boss magana dukda there is so much to tell. Washegari ta kasance thursday ‘yan garin Maiduguri kap angani kuma an karanta a news cewa Flames Enterprises suna neman masu aikin had’a coffee. Zokuga yadda maza da mata suka taru bakin building na Anas yau. Da k’yar yasamu passage. 10-10 ake d’ibansu ake kaisu kitchen kowa da coffee machine dakuma ingredients na had’awa. First set suna gamawa Mr. Fauzi ya sauk’o tasting na wanda yafi masa dad’i seya samu aiki ya maye gurbin Fannah dan ko bacci ya kasa jiya se tunanin coffeen Fannah yake duk yadda yayi ya mance coffeen Fannah ya kasa, he is addicted to it dak’yar yasamu yayi bacci bayan syrup dayasha. Yana kai na farkon baki ya mayar cikin cup d’in “meh wannan? Ruwan wanki ko meh? take her out.” “Yes Sir” cewar Adam. Nan na biyu ta matso itama yana kaiwa baki ya mayar cikin cup d’in “ke kinma san meya kawo ki nan kuwa? Take her out.” “Yes Sir.” Na uku ma takawo nata shima yana kaiwa baki ya miyar cikin cup d’in. “Take her out bana san sake ganin fuskarta.” Haka de bayin Allah suketa shigowa anayin round-round, na mutane 25 maza da mata Anas ya tab’a dukka ba wanda ya masa koda kusa da na Fannah ne. “Fire them all, duk ka koresu bana san sake ganinsu. Fire them now!” Yaja tsuka sannan ya shiga elevator’nsa ya haura zuwa office. A ranan yayi firing ma’aikantansa guda biyar plus na jiya abin de ba dad’in ji. Hankalin kowa tashe yake abu kad’an kayi a danna maka fire. Yau yini biyu kenan Anas be sha coffeen Fannah ba amman ji yake kamar shekaru aru aru ne. Yarasa ina ze sa kansa, abinci ma ba sosai yake ci ba koda ya gwada had’a coffeen baya masa dad’i bai ma iya sha gashi wannan karan ko Shettima ma be sanar dashi abinda ke damin sa ba kamar yadda ya hana Amal ma. Kawai in an tambayesa cewa yake rasuwar Baba (Mr. Muh’d) ya tuna. Yau k’imanin sati kenan da barin Fannah aiki gun Anas, k’imanin sati be d’and’ana coffeen ta me dad’i a bakinsa ba. Ba yadda beyi ba dan mancewa da coffeen nata amman yakasa shi daga baya nema yagano ba coffee natan kad’ai yake missing ba ita kanta Fannan ma missing nata yake, yes yayi missing Fannah, yayi missing innocent face nata, yayi missing kukanta dakuma muryarta me dad’in gaske, yayi missing kamilallen shirinta na kullum, komai yayi missing akan Fannah. Yabi ya k’osa next week ya iso ya kira Manager’n FCB ltd. Fannah kuwa rayuwarta ta juma batayi dad’i kamar yadda take ba yanzu, ba ruwanta da wani tashin hankali, aikinta tana yinsa me kyau ba ruwan asst. Manager’n ta da shiga harkar mutum bale ma ya mata masifa. Sosai take jin dad’i aiki wajen. Amal kuwa duk da erin warning da Anas ya mata ta kasa dena kiran Fannah saboda hankalinta. Wannan shine karo na farko da take sab’awa umurnin Anas. *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:49, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 2⃣9⃣ “Kasan Fannah Aleeyu ko wacce ta tab’a aiki anan?” “Wacce take had’a maka coffee Boss?” “Yes ita.” ya amsa sa a takaice. “Sosai nagane ta friend na Yusuf ce.” “Toh ban tambayeka ba.” Ya tsawata masa. “I’m sorry” Boss ya sunkuyar da kansa. “You better be, bawani aiki zan baka ba illa spying akan Fannah dana keson kana min, inasan yazamo duk inda zataje dakuma duk abinda take ciki ka sani kana turo min rahoto.” “Okay Boss nagane.” “Good, karka bari ko da information d’aya ne ya wuce ka, do you get me?” “Yes sir.” “Good inka min wannan zan baka mak’udan kud’ad’e. Off you go, ga number’nta” nan ya mik’a masa rubucaccen number’n Fannah kan wata paper. “Ka kirata yanzu seka samu kayi tracing inda take.” “Yes Sir” nan ya fice. _30 minutes later..._ “Hello Boss yanzu Fannah tabar state secreterial.” “Good ka shiga ka tambaya min ko aiki suka bata” “okay sir.” Nan ya katse wayar ya shiga. Tambayoyi yariga ma receptionist na wajen itako jaka ta riga basa information saboda tagansa kyakkyawa ba laifi, dama da biyu Anas yayi assigining Idrees yin aikin. “Kina nufin har kunbawa Fannah aikin kenan?” Idrees ya tambayeta. “Eh Idrees mun bata saboda takardun ta sunada kyau.” Ta fad’a ta na kashe masa ido “Okay inasan number’n Manager’n ku if possible.” “Sure Idrees” nan ta basa dan sokanci godiya ya mata sannan ya fice “se na kira ki koh?” “Okay!” tace masa tana nin dad’i. Aiko yana fita yayi blocking number’nta bata sake ganinsa ba tun daga ranan. Anas ya kira “hello Boss nayi tambaya wai eh tasamu aiki a ma’aikatan amman na amso maka number’n boss d’in sekuyi magana.” “Excellent! Ka iya aiki” yayi exclaiming “turo min lambar and kacigaba da binta aikinka na kyau.” Bayan minti d’aya Idrees ya masa sendn number’n Manager’n wajen. Da telephone office nasa ya kira Manger’n. Manager’n na ganin Flames Enterprises ya d’aga jiki na rawa. “Ranka ya dad’e Mr. Fauzi ina gaisuwa.” “Yawwa barka” straight to the point ya wuce “Fannah Aleeyu da kuka bawa aiki yanzu nakeson kuyi firing nata.” “Amman Si-” Katse sa Anas yayi “zan baka dubu d’ari biyar.” “Toh anyi an gama Sir bari in ta dawo gobe ina jiran alert.” “Karka damu just do as I say ina jiran feedback.” Idrees be bar bibiyar Fannah ba sanda yaga tashiga gida sannan ya kira Anas ya fad’a masa. Fannah ta shiga cikin gida da farin ciki fal a ranta ta sanar da family’nta aikin da ta samu sosai suka tayata murna. Washegari ta koma ma’aikatan suka tareta da sad news na fasa bata aikin da sukayi. Zuciyarta taji ya kariya. “Dan Allah kode wani abun nayi kuka hana ni aikin kuyi hak’uri, ina buk’atar aikin nan. Kefa jiya kika kai wa Manager’nku takardu na yakuma yaba, yau kuma kice kun fasa?” “Eh an fasa seki k’ara mai please.” Abin tausayi Fannah taja jakarta ta fice wani ma’aikatan ta wuce neman aiki take suma suka bata aiki. Bayan tafiyarta aka koma gidan jiya Idrees yabi sahu yau ma mace yasamu as receptionist d’in ya tsarata yasamu ya ta fad’a masa news dayakeso tare da basa number’n Manager’n. Shima kud’i da dama Anas yabasa ya yarda yayi firing Fannah. Duk aikin da Fannah ta samu da ta koma washegari se suce sun fasa sun canza mind nasu, sosai abin yake daminta ranan harda kuka. A inda tasamu aiki a k’arshen ne bayan tafiyanta Idrees ya shiga to his suprise yaga wani santalelen gardi as receptionist d’in yasan koda mutuwa zeyi ba basa information da yakeso ze masa ba. Fita kawai yayi ya kira Anas nan ya masa kwatancen ma’aikatan. Meeting Anas yakeda amman yayi cancelling in akan Fannah da coffeen ta ne baya wasa. Bayan like 15 minutes Anas ya iso wajen tare suka shigo cikin building d’in atare wajen receptionist d’in suka nufa. Bayan ya gaishesu Anas yace, “take me to your Manager.” “Sir I'm sorry amman se in kanada appointment dashi tukuna, me sunanka in duba.” “Tambaya ma kake waye shi? Bakasan Mr. Fauzi bane?” Cewar Idrees dake tsaye bayan Anas. “I’m sorry Mr. Fauzi amman bakada appointment dashi.” “You’re very stupid and zan tabbata an koreka daga aiki anan stupid kawai” Chan ya hango wani na wucewa “hey!” Ya danna masa kira jiki na rawa mutumin ya iso “ranka ya dad’e, sannu da zuwa yau manyan bak’i mukeda a office namu? Kai D’anladi bakasan mutane bane? Ai Mr. Fauzi ba’a had’a masa appointment. Koda yaushe yazo he is welcomed” “Ahto gaya masa de” cewar Idrees. Kallo Anas ya watsa ma D’anladin sannan ya dawo da kallonsa kan Isah “so nake ayi firing wannan mutumin.” ya nuna D’anladi da yatsa. Hak’uri Isah ya soma bawa Anas. “Mr. Fauzi dan Allah kayi hak’uri shekaran jiya ya shigo gari, be sanka bane, kai D’anladi baraka basa hak’uri bane?” Ya daka wa D’anladi tsawa. “Kayi hak’uri Sir.” Kallon sa Anas yake cike da rashin isa “sede D’anladin kam. Uhm Isah Mr. Abdullahi na nan kuwa?” “Eh Manager na nan mu haura sama please.” Nan sukayi sama kamar yadda Anas ya saba siye mutane da kud’i haka ya siye Mr. Abdullahi. A dad’insa yanzu kap inda Fannah zata samu aiki yayi blocking batada wata option other than ta masa aiki. **** Kuka Fannah take sosai Mami na bata hak’uri. “Haba! Fannah sekace ba muslima ba? Ke da nasanki da rungumar k’addara kiyi shiru kukan ya isa.” “Haba Mami abin ba daidai ba, ace duk inda naje se bayan sun d’aukeni in nakoma washegary kuma suce sun fasa.” “Ya isa Fannah akoi Allah ki dad’a hak’uri.” “Kiyi hak’uri Ya Fannah” cewar Afrah tana bubbuga bayanta a hankali cike da tausayi da damuwa. Fannah bata sake lek’a waje ba tun daga ranan. Sosai rashin aikinta yake damunta in kud’in hannunta ya k’are bata san ina zata samu kud’i tabiya kud’in asibiti da magunan Baba ba. Tasan sarai inda a yanzu zata je wajen Anas ze bata aiki amman barata iya jure wulak’ancin sa ba, mutum ne ace ko kad’an baida slightest regard wa d’an adam. Ita dashi har abada in shaa Allah ta gommaci talauci ya kashe ta data sake masa aiki. _One week later..._ Haukacewa ne kawai Anas beyi ba yarasa me ke ajiye Fannah har yanzu batazo neman aiki gunsa ba. Gashi koya tura Idrees ce masa yake Fannah bata fita, toh why? Ta hak’ura da neman aiki kenan komeh? Bare iya explaining ya yayi missing coffeen ta ba tun rananda tabar masa aiki har ila yau baicin abinci kamar yadda ya saba ci da. Shi yanzu abu d’aya ne yasan inya aiwatar dolen Fannah zata dawo masa aiki shine in zeje gidansu, gashi dama Idrees yamasa bayanin yadda gidansu Fannah yake basuda arziki. Wayarsa ya d’auko ya kira Ahmad. “Hello Boss good day.” “Yawwa kaje ka d’au credit card d’ina cikin mota a bud’e ne kayi duk siyayyan dakasan magidanci zeyi wa family’nsa I mean food items, kayan sawa home appliances komi da komi ka gane?” “Yes Boss angama.” Nan ya katse wayarsa. “In baraki dawo ba Fannah I will force you to.” _5 hours later..._ Anas na zaune a office nasa yana jiran call daga Ahmad baya son se Maghrib yayi, aikuwa a lokacin Ahmad ya kirasa “Hello Boss komai is in place kamar yadda ka buk’ata motan kayan na nan pake a bakin main gate.” “Good gani fitowa.” Turare ya sake feshe jikinsa dashi ya giara gashin kansa ya tabbata he is looking okay sannan ya fice. Motarsa ya shiga motan kayan kuwa Ahmad ne ciki yana gaba Anas na biye dashi har gaban gidansu Fannah suka tsaya. Sosai yasha mamaki ashe saisa Fannah batta wasa da aikinta ashe basu da k’arfi ne sosai. Kallon gidan ya tsaya yi dan ko a Bama gidansu yafi wannan kyau. Daidai lokacin Aiman ta taso daga islamiya se b’antare charbin Malam dake hannunta take tana nufowa kusa da gidan alokacin data d’aga fuskarta Anas yaga alaman kamannin Fannah tattare da ita nan take ya yanke hukuncin kasancewar ‘yar yarinyar k’anwar Fannah. Daidai tazo shiga gidan ya dakatar da ita ta hanyan kiran ta da “‘yan mata.” A hankali ta d’ago kai tana kallonsa bata gane kamanninsa ba kasancewar yasa sunglasses. “Wace ‘yanmatan” ta kalli left and right “ni? Barin d’an maka tambaya bature ne kai please naga kayi fari dayawa” Dariya sosai Anas ya tsaya yi sekace ba shi ba, kawai se yarinyan ta tuna masa da Angel nasa Amal. “ A’a ni ba bature bane ‘yanmata” “ Nifa kadena cemin ‘yanmata, ai Ya Fannah tace ni yarinya ce ba ‘yan mata ba wai ita da Ya Afrah ne ‘yan mata.” “Toh Ya Fannah ta miki k’arya ai ‘yan mata ce ke.” “Toh kaikuma fa? Samari?” Ta tambayesa tana jefa charbin malam data b’are a baki tare da taunawa. “Ni big uncle ne suna na Anas, kinacemin Ya Anas.” “Ya Anas.. Ya Anas ni Aiman a ina na tab’a jin wannan suna?” Ta tsaya tana tambayar kanta. Yana ciro glasses nasa aiko kamanninsa ya bayyana. “Laaaaa!!! Blue eyes na TV. Me kazo yi agidan mu? Ashe ba bature ne kai ba, kazo ne muma asamu a TV’n?” Dariya sosai yake wanda ya mugun masa kyau, fararen hak’waransa suka bayyana, dimple nasa d’aya ya lotse. “Kinasan kiga kanki a TV?” “Eh mana ai social studies teacher’n mu tace celebrities kawai ake gani a TV nima inasan in zama d’aya.” “Toh kar ki damu, yanzu kizo ki kaini cikin gidanku.” “A'a'a'ahhhh chabdi! Ai Ya Fannah ta hana. Maza basu shiga gidanmu gaskia me blue eyes kayi hak’uri karka sace min iyaye da yayu. You are a stranger.” “Kefa kikace kina gani na a TV karki damu b abinda zan miki. Ahmad ina sweet d’incan?” nan Ahmad ya koma mota ya ciro packet na sweet Anas ya amshi, “ungo zo ki karb’a.” Ya fad’i yana mik’a mata. “Blue eyes tsakanin ka da Allah baka sa abin sace yara ciki ba?” dariya sosai Ahmad yake. “Kice min Ya Anas ba blue eyes ba.” “Toh Ya Anas.” Ta fad’a yawunta na d’iga k’asa. “Bari kiga” nan ya bud’e ya ciro d’aya tare da sha “kinga ba abinda yamin. Zoki karb’a se ki kaini gidanku. Ya Fannah tasanni, nine Mr. Fauzi. ” “Ohhh ashe kaine me sa Ya Fannah kuka.” Yi yayi kamar be jita ba yace, “karb’a mu shiga toh.” Ba musu ta amshi pack na sweet d’in “muje toh Ya Anas.” Bayan ta yabi suka shiga gidan kam ba laifi tsatsaf ba k’azanta. “Mami! Ya Fannah! Ya Afrah! kufito munyi bak’o kuma ya bani sweet har packet.” Fannah ce ta soma fitowa ko hijabi batada ‘yar vest ne kawai jikinta tana shan iska. “Aiman ban hanaki shig-” bata k’are maganar ba suka had’a ido hud’u da Anas ai a guje ta koma ciki se nishi take. K’wak’walwar Anas sanda yabar functioning na d’an lokaci ganin Fannah ba kayan arziki. “Ke Ya Fannah wa kika gani haka kike wannan nishi” cewar Afrah dake game as always. Kasa magana Fannah tayi kawai waje take nuna mata da hannu. “Meh gamo kikayi?” Kai ta kad’a mata still tana nuna waje. Kafin Afrah ta tashi suka jiyo muryan Mami na masa lale su Mami anga Mr. Fauzi. Lek’awa Afrah tayi tagansa zaune kan tabarma d’aya da Mami. Ashe haka bawan Allan keda kyau, yama fi kyau a fili akan a gidan TV lallai Allah yayi hallita. “Ya Fannah Mr. Fauzi nefa! Mr. Fauzi a gidanmu!” ai da gudu tayi wajen sa kayansu taciro kayan sallarta. “Ki sa hijabi mu fita mu gaishe sa. Ma meyazo yi tukun? Halan bikonki” Duk ta kidime se suratai take tayi. Hannunta Fannah ta rik’o “ke jakar ina ce? Ina zaki? Meh Mr. Fauzi yazo yi gidan mu? Nashiga uku Allah sa ba sharri ya taho dashi ba.” Afrah ta bud’e baki zatayi magana suka jiyo kiran Mami “Fannah! Afrah! kufito mana Mr. Fauzi nefa yazo.” “A’a Mami Anas de” cewar Anas sewani behaving yake kamar d’an arziki. “Kufito da sauri” Mami ta sake k’olla masu kira. “Toh” Afrah tace. “Ya Fannah kiyi sauri.” “O’o ni barin fita ba ni yama yasan gidanmu? Ya Allah help me!” Hannunta Afrah ta fisga daga rik’on Fannah ta fice a guje har k’asa ta gaishe da Anas ya amsa da fara’a se murmushin show off yake. “Aiman kawo wa Ya Anas ruwa kinji?” “A’a Mami ta bari daga office nake yanzu naci abinci.” “Allah Babana ko ruwa bara ka sha ba?” “Eh Mami, ina Baba? Ya jikin nasa?” Fannah dake mak’ale jikin window tana jinsa ji take kamar taje ta shak’uresa ji yadda yake abu kamar d’an arziki. “Jikin Baba da sauki. Afrah ina Fannah newai? Fannah!” Ta danna mata kira. “Na’am Mami” ta amsa kan wanda zatayi kuka. “Kifito mana me kikeyi ne?” “Mami gani nan.” Hijabi ta zumbura sewani kumbure kumbure take. Koda ta fito bata d’aga kai ta kalli Anas ba shikuwa idanunsa na kan ta rabuwansa daya sata a ido har ya manta. “Baki ga Mr. Fauzi bane da baraki gaishe sa ba?” yi tayi kamar bata ji me Mami tace ba. *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:49, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 3⃣0⃣ Kallon Fannah Mami ke cike da mamaki, wannan ne karo na farko da Fannah ta sab’a wa umarninta bakuma tare da ta nuna damuwa ba. “Fannah dake fa nake magana, meke damunki ne? Baraki gaishe sa ba?” Ta sake tambayarta. Nan ma shiru tayi, a kunyace Mami tace, “Anas kayi hak’uri bansan meke damun Fannah ba.” Murmushi yake kaman ba shi ba “ba komai Mami maybe bata san yin magana ne” blue eyes nasa ya d’ago yana kallonta sosai, haka kawai yasamu kansa cikin niahad’i in yana kallon innocent face nata, sarai taji yadda yake kallonta amman ko d’aga kai batai ba. “Fannah tunda baraki gaisheni ba ni zan gaisheki ina wuni?” Shiru tayi bata amsa ba, Mami de tashiga cikin duhu wai ace Mr. Fauzi na gaishe da Fannah amman barata amsa ba. “Anas kayi hak’uri dan Allah bansan meke damun Fannah ba yau, Afrah ko kunyi fad’a ne?” “A’a Mami ba abinda ya had’a mu.” Afrah ta fad’i cike da zumud’i se satan kallon Anas take. Giaran murya Anas yayi “uhm Mami nasan kuna mamakin ko me nazo yi anan koh? Bikon Fannah nazo yi, dama misunderstanding muka samu tabar min aiki akan had’a coffeen da take min ne tace ta gaji dayi sede in zan bata aikin daya fisa nikuma alokacin banida aikin da zan bata.” Baki wangalau Fannah ta bud’e tana kallon ikon Allah yanzu ko kunya baiji yake wannan k’arya. Kut lalle! “Mami walla-” ta gwada kare kanta. Katse ta Mami tayi “se yanzu bakin ki yaga daman bud’uwa Fannah? Toh kiyi shiru Anas ya gama, ina jinka Baba na.” Idanun sa ya d’aga yana kallonta, itama kallon nasa take, murmushin mugunta ya saki mata wanda ta murgud’a masa baki in return tare da kawar da kallonta daga garesa. “Yawwa, shine tayi resigning amman yanzu da nake neman Personal Assistant (PA) kuma gashi takardun ta sunada kyau zan d’auke ta aiki. Albashi dubu d’ari biyar da kuma weekly allowances N5,000.” “Alhamdulillah!” Mami ta fad’i cike da murna. “Alhamdulillah! Aiki har gida Allah ya kawo miki Fannah, wallahi Anas ba abinda zance sede Allah maka albarka ya k’ara d’aukaka da girma, aiki ba inda Fannah bata nema ba amman seta koma washegari se suce sun fasa, abin de ba dad’i” “Fannah ke baki iya godiya bane?” Mami ta tambayeta. Shiru tayi kamar bata jita ba. “Mami kibar Fannah yau kawai bata san magana ne, ai mutane yanzu sun sa san kai a gaba, su yasu kawai suka sani. Se hak’uri.” Idanunsa ya d’aga yana kallon Fannah dake tsaye har yanzu ta had’e gira gu d’aya. “So Fannah zaki dawo min aikin? Tunda na canza miki post yanzu” “Anas yanzu har seka tambaya ko zata koma ne? Ai komawa ta riga ta koma kawai ka fad’i yaushe kakeson tayi resuming office.” “Mami!” Fannah takira sunanta cike da takaici. “Wai me haka?” Sanyi yaji a ransa jin muryarta kawai. “Eh mana Fannah, a jinki akoi inda zaki samu aiki me kyau haka ne? Gaskia Anas mungode sosai sosai Babansu na bacci da ya maka godiya shima.” “A’a Mami ba komai nine da godiya. Gobe nakeson Fannah ta soma aiki.” “Allah kaimu Anas, In shaa Allah a goben zaka ganta” Hannu yasa a aljihu ya ciro bandir na d’ari biyu tare da ajiyewa gaban Mami “ga wannan a saya wa Baba magunansa dashi da kuma sweet wa Aiman ko?” ya dawo da kallonsa kan Aiman dake manne a jikinsa se mamakin gashin hannunsa take. “Yeyy! Ya Anas nagode. Ya Fannah ba sekin sake min rowan naki ba Ya Anas yace a siya min” kallo Fannah ta watsa mata wanda batasan Anas na kallonta ba. “Anas Babana da wahala haka? Toh mungode Allah saka da alheri.” Fannah ji take kamar ta k’urma ihu ita wallahi barata koma masa aiki ba sede sama da k’asa su had’u. “Ermmm Ahmad!” ya danna masa kira nan Ahmad dakw waje yashigo bayan ya gaishe dasu Mami Anas yace ya shigo da kayakin. Dama already yariga ya tara almajirai nan suka soma shigowa da kayaki. Ba Mami kad’ai ba har Fannah sanda tasha mamaki wato siye mata iyaye zeyi da kud’i da kayan duniya, lallai kuwa. Kap tsakar gidansu sanda aka cika da kayaki tun Mami da Afrah suna godiya har suka gaji sukayi shiru. Addu’a sosai Mami ta riga ma Anas tana suburbud’a masa albarka ga kyautan kud’i ga kuma na kaya, abinde ba’a cewa komi. “Anas kace ko ruwa baraka sha ba? In aika Aiman ta siyo maka ko maltina mana.” “A’a Mami ba komai” “Gaskiya Anas ba abinda zance maka, ka gama mana komi naso ace idan Babansu biyu wallahi yamaka godiya, Allah saka da alheri ya k’ara bud’i” “Haba! Mami ai ba godiya tsakaninmu, ya isa please.” “Toh ina zuwa, Afrah biyoni.” “Afrah kad’ai Mami nikuma fah?” Cewar Aiman “ni ma sena bi ku.” Cak ta tashi daga gefen Anas ta bi bayan su Mami zuwa d’akin Baba. Ya rage daga Anas se Fannah itama juyawa tayi zata shiga d’akinsu ya mik’a dogon hannunsa ya cafko ta da hijabi chak ta tsaya ba tare da ta kalle sa ba tace, “Mr. Fauzi ka sake min hijab.” K’in sakewa yayi, ya mik’e tare da shan gabanta yana d’auke dawani murmushin mugunta a fuskarsa. “Stop pretending, nasani you miss me.” Yace da ita. “Miss you? A dalilin me zanyi missing mutumin da yake sa ni kuka all thetime? Mr. Fauzi kasan meh? Ni barin sake koma maka aiki ba, na bari na bari forever, ko coffee maker’n ka barin sake zama ba bale PA, kuma wannan tarukucan kayakin daka kawo ka tattara ka mayar dasu inda ka kwaso su bama buk’ata.” “Ai aiki min kin riga kin dawo k’arfe 8:00AM gobe don’t be late, wannan kayaki kuma anan zasu zauna, tunda kikayi resigning ba tare da kin sanar da ni ba nima haka zan dawo dake ba tare da sanin ki ba. Karki manta everything can be bought with money kamar yadda na saya family’nki yanzu. Inba wai so kike ki b’ata wa Mami rai ba zaki dawo min aiki gobe.” “No Mr. Fauzi you are wrong, not everything can be bought with money, aiki maka kuma na riga na bari ba dawowa.” Hijabin ta ta fisge tashiga ciki. Murmushi yake sosai danko yasan definately yes Fannah zata dawo masa aiki, ya riga ya saye Maminta. Bada jimawa ba Mami ta fito dawani farin handkerchief me flower a hannunta. “Yawwa Mami zan tafi kar Maghrib yamin anan, in Baba ya tashi a gaishesa please.” “Da wuri haka Baba na? Toh mungode fa sosai, in shaa Allah zan fad’a masa. Ga wannan ba tsada amman naji yakamta in baka wani abu kaima da abinda ka mana.” Hannu yasa ya amshi, “thank you Mami, nagode sosai ai ba tsadar abu ne yadamu ba value nasa ne. Aiman, Afrah na tafi.” Baki na b’ari Afrah tace, “mm..mungode Mr. Fauzi Allah kare hanya.” “Ameen” yace. “Ya Anas yaushe zaka sake zuwa nima asani a TV?” “Very soon Aiman” ya amsa ta yana murmushi. “Mami ki tunawa Fannah k’arfe 8:00AM gobe kar ta makara please. ” “In shaa Allah Anas karka damu a gaida mutan gida. Fannah! Fannah! Zo ki raka Anas mana.” Yana jin haka ya rage saurin tafiyar sa yasoma tafiya a hankali. Fannah daka lab’e jikin window ji take kamar ta kashe kanta ta huta wato handkerchief da tunba yau ba take bin Mami ta bata tak’i amman ta kama ta bawa Mr. Fauzi, dakyau ta kyauta. “Fannah!” “Na’am” ta amsa. “Kifito mana.” Tana zumbure zumbure tafito “gani” tace tana kallon k’asa. “Bakiji Anas ze tafi bane? Wuce ki raka sa.” “Mami!” Tace kan wanda zatayi kuka. “Ki wuce nace” Mami ta bud’e mata ido. A sanyaye tabi bayan Anas yanajin footsteps nata a bayansa ya sakar da murmushin mugunta. Bayan sun kai bakin k’ofa ya juyo ya kalleta, kallonta ta kawar daga garesa “zaki iya komawa, kinsan rules d’ina bana tolerating late coming.” Can k’asa tace, “damuwanka saboda ni ba aiki zan dawo maka ba.” “Haka kikace? Se mugani.” Nan ya shiga motarsa ya fice bayan ta dawo ciki ta tarar da su Mami se bud’e bud’en ledoji suke ji take kamar ta tattara kayakin ta k’ona har ta kai da shiga d’aki Mami ta kirata “zo nan Fannah.” A sanyaye ta juya “gani” tace. “Kin kyauta min kenan yau? Ba se Anas d’in yace ban ba ki tarbiyya ba.” “Ba seya che d’inba” tace can k’asa k’asa aikuwa Mami ta juyo ta “aww abinda ma zakice kenan yace d’inko? Ni bansan me ya shige kiba yau Fannah, keda ya kamata kiyi murna ki gode wa Allah har gida Anas yazo yayi bikon ki amman kike wannan rashin hankalin? Kiga alkhairun daya mana, haba Fannah.” “Mami ni barin koma masa aiki ba gaskia, zan cigaba da neman wani.” “Ya Fannah mesa?” Cewar Afrah dake k’ok’arin bud’e leather’n set na comb. “Bansani ba kema k’aramar munafuka sekace baki san halin Mr. Fauzi ba. Wallahi Mami kullum seya sani kuka sede in banje office nasa ba ni gaskia banaso.” “Ji zancen banza dukanki yake ne?” “A’a amman yata min masifa yana daka min tsawa.” Cike da mamaki Mami ke kallon Fannah. “Wato har yanzu baki bar halin ki na kuka da an d’an miki magana ba koh?” “Ai Mami magana daban masifa daban ni gaskia barin koma wa Mr. Fauzi aiki ba.” “Shikenan Fannah, kin mana k’ok’ari ai dama dole wataran ki gaji, mungode. Da kud’in da Mr. Fauzi ya kawo zanyi k’ok’ari in nemowa Afrah polythecnic itama, inda hali ma zan ma Mr. Fauzin magana ya cika min sauran tunda ke kin gaji.” “A’a Mami niba abinda nake nufi ba kenan.” “Toh me kike nufi Fannah? Aiki har gida a kawo miki da albashi me kyau amman kice bakiso? Me kike nufi toh Fannah?” “Hummm yi hak’uri Mami” cewar Afrah. Wani kallo Fannah ta watsa mata k’anwar shed’an kawai ta fad’i a zuciya. “Afrah ‘ya ta, Fannah ta gaji damu ki dage kema kiyi karatu zan nema miki babbar makaranta.” Fannah batasan nayi ba kuma again tasan halin Mami sarai in ta kama surutu bata gajiya in bawai yanzu ta karb’i aikin Mr. Fauzi bane shikenan zasu b’ata ga Afrah k’anwar shed’an abinda takeso kenan. Da k’yar tace, “Mami kiyi hak’uri dan Allah ni ba abinda nake nufi ba kenan. Gobe zan fara zuwa aikin in har it will make you happy.” “Toh ko kefa Ya Fannah?” cewar Afrah. “Afrah kinga kimin shiru ba ruwanki.” Matsowa tayi kusa da Mami. “Mami kiyi hak’uri.” “Haba Fannah keda kullum nake yaba hankalinki. Shi masifa haka Allah yake halittan wasu mutane dashi, ko magana suke maka sekaji kamar masifa ne. Kekuma sekiyi hak’uri Anas nada kirki ba kowani Boss bane zezo yayi bikon ki musamman ma da kika bar masa aiki saboda kin raina post daya baki.” Fannah ta bud’e baki zata k’aryata hakan kawai tayi shiru dan there will be no point Mami ba yarda zatayi ba. Nasiha sosai Mami ta mata kan tana hak’ura da halin Anas na masifa is not easy ace d’an shi yana running babban Enterprise irin Flames Enterprises. **** Fannah duk tashiga tashin hankali, tana nata Allah na nasa. Ita gabad’aya ta riga ta cire Mr. Fauzi daga ranta a cewarta ba abinda ze sake had’a ta dashi se gashi wai zata koma masa aiki bama as coffee maker ba personal assistant yadda kulum *_TANA TARE DA SHI_* Ta b’angaren blue eyes kuwa tun barin Fannah aiki be sake samin kwanciyan hankali da nishad’i kamar na yau ba. He can’t wait ta had’a masa coffeen ta me uban dad’in gaske already ya riga ya sa an wanke masa manya manyan flasks guda biyu da zata cika masa cikinsu dashi. _Washegary..._ Tun k’arfe bakwai saura 6: 40AM Mami tazo ta tada Fannah tasata wanka ta mata breakfast da kanta, d’aya daga cikin ready made hijaban da Anas ya kawo musu Mami ta zab’a mata d’aya sam Fannah tace barata sa ba, tayi k’arya wai batta san kalan haka Mami ta barta tagama shirinta cikin baby pink. Kwalli, lip gloss da powder kawai ta sa ta d’au jakarta ta fice bayan Allah kare da Mami ta mata. Takwas saura minti biyu ta sauk’a daga keke napep. Tana shiga suka ci karo da Yusuf had’iyeta ne kawai beyi ba dan murna, finally aiki ze dawo normal kamar yadda yake da. Gaisuwa kad’an sukayi dan kar ta makara sosai Mr. Fauzi yasamu abin surutu kai. 8:03AM tashiga office nasa tsaye ta samesa da wata staff yana bata orders bayan d’an lokaci ta fice ya rage daga Fannah se Anas. Sanye yake da pitch shirt da ocean blue neck tie, suit nasa na rataye kan hanger. Ganin bata da niyan magana yace, “baki iya gaishe da Boss naki bane?” Ba tare da ta kallesa ba tace, “good morning.” Be amsa ta ba ya koma kan kujera ya zauna tare da kirawota steps kad’an tayi sanda ta iso gaban table d’insa ta tsaya. Magana yake sekace ba shi ke murmushi da dariya jiya ba. “So kamar yadda kika sani you’re now my personal assistance, right?” Kai ta giad’a a hankali. “Good incase kin manta rules d’ina zan making miki clear yanzu.” “Banasan body language in na miki magana dole kema kimin Banason shisshigi. I don't tolerate late coming. Ke PA na ne yanzu meaning a koda yaushe muna tare amman hakan be baki daman kina kallo na anyhow ba. Don’t fall for me in the process, dan ko kin soni ni baran so ki ba.” Har tsakiyan kanta ta jiyo wannan kalamu, dan wannan zagi ne. “Ki mayar da hankalin ki sosai wajen aiki, banasan aiki da mistake always. As my PA duk abinda nace kiyi shi zakiyi ba objection ba musu. Hiran da kika saba zuwa yi da Yusuf has to stop, in an tashi daga aiki sekuje ku cinye kanku. Normal lokacin tashinki k’arfe 4:00PM ne amman in aiki yayi yawa I might hold you. Na k’arshe obey all my rules. I hope am clear?” Ya tambayeta “Yes you are amman ka kwantar da hankalin ka Mr. Fauzi ni barin tab’a san mutum me hali irin naka ba, kuma Yusuf ba saurayi na bane.” “Incase ban fad’i wannan part cikin rules d’ina ba let me now. Banasan kina fad’a min magana duk abinda nayi ko na ce ko be miki ba, koba haka yake ba you have to accept it.” Lallai ma! Mamaki sosai ne ya cika Fannah wato dalilin dayasa ya dawo da ita aiki kenan saboda yana cin mutuncin ta. *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:50, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 3⃣1⃣ “Am I clear?” Ya tambayeta. “Yes” tace murya chan ciki-ciki. “Good” daidai lokacin wayarsa ya soma ringing take ya d’aga “okay I’m on my way.” Ding! ya katse. Suit nasa ya jawo yasa yasake feffeshe turare jikinsa, Fannah duk tana tsaye ko kallon direction nasa batayi bale ya chakka mata magana. Wayoyinsa ya kwasa “follow me” yace da ita. A sanyaye tabi bayansa ganin ya nufa wajen personal elevator’n sa yasa ta juya dan bin na public kafin ya mata wani rashin mutuncin, duk abinda tasan ze jawo masu matsala k’ok’arin kiyaye sa take. Sanda ya bud’e yashiga elevator’n sannan yayi noticing Fannah bata biye dashi chan ya ganta tana nufan gun d’ayan elevator’n. “Miss Aleeyu!” ya kira sunanta a tsawace chak ta tsaya tare da juyawa. “Baki ji me nace bane? I said follow me.” Ya sake nanata kansa. “Sir-” bata k’are maganar ba ya katse ta “acikin rules d’ina na fad’a miki banasan muna musu.” Kanta sunkuye ta je ta samesa tana shiga ya rufe elevator’n, daidai nan wayarsa ya soma ringing daga side pocket na suit nasa, yana ciro wayar number ya bayyana kai bayan yayi nazarin wake kira ya d’aga danko baya saving number’n ‘yan mata a wayansa in bawai ta kama ba “hello Salmah?” “Cute eyes, ya kake?” tace dashi “Lafiya” ya amsa ta. “Cute eyes godiya nake son sake maka, dress daka kawo min ya had’u sosai, thank you.” “Don’t mention hun, zani meeting yanzu zan kiraki later.” “Okay cutie.” Nan yayi hanging. Fannah dake sauraransa kai kawai ta kad’a, dan aikinsa kenan a ‘yan satukan data masa aiki kwanaki bata san ‘yan mata nawa yayi dumping ba. Tsantsan so yake nuna masu na ‘yan kwanaki yana gaining trust nasu seyace suyi break up, ita ta rasa wani erin player ne Anas. Elevator’n na bud’uwa ya sa kai ya fita itama haka tana biye dashi. Wajen da ake ajiye masa key ya nufa chan yama driver’nsa magana dan yau baya jin driving. Bayan sun isa wajen motar nasa driver ya bud’e masa k’ofa “enter” yace da Fannah. Cike da mamaki take kallonsa kamar ya enter ina yakeson kaita? Katse mata tunani yayi, “incase kina wondering ko zan kaiki cin abinci ko shopping ne you are mistaking, you are my PA duk inda zanje dake zanje so get in.” Miyau ta had’iye ta shiga ta wuce can k’arhen gefen motan a yayinda shima ya shiga. Haka kawai taji zuciyarta na bugawa duk sanda ita da Anas suke kusa da juna se tana jin wani eri ba dad’i. Bayanin inda zasu yama driver’n a hankali ya soma tuk’i. Ita Fannah ta rasa wani erin san AC Anas yake, hijabi ne a jikinta amman sanyi takeji, hijabin nata ta duk’unk’une dan sanyi, ganin haka Anas ya saki murmushin mugunta ta gefen da dimple nasa yake. “Moosa ka k’ure AC’n zafi nakeji” “Okay Boss.” Nan ya k’ure tas! take motan ya d’au wani irin mahaukacin sanyi kallonsa Fannah ta tsaya yi, wato ya gane sanyi takeji shine dan mugunta ya k’ara, ita ba ma wannan ba, duk sanda tasha sanyi sosai pneumonia’n ta tashi yake tun lokacin da akayi raping nata a Bama ruwa ya mata duka take fama da pneumonia tashi tashi. “Don’t break my rules nace miki banasan kallo dayawa.” Bata ce masa komi ba ta kawar da kanta dakuma sake duk’unk’une kanta cikin hijabin. Kansa ya jingina jikin kujeran tare da rufe ido bada dad’ewa ba wayar Anas ya soma ruri ganin wa ke kira ya d'aga da sauri “hello an samun?” “Yes sir ga details d’in.” Cewar mutumin “Okay d’an tsaya please let me get a paper” Juyowa yayi ya kalli Fannah, “ina jotter’nki?” “Jotter kuma?” Ta tambayesa cike da rashin fahimta. “Hold on please” yace da mutumin da suke waya sannan ya dawo kallon sa kan Fannah “yes you are my PA ya kamata duk inda zakije yazamto akoi paper da pen a tattare dake saboda kina jotting down abubuwan da nake buk’ata.” “I’m sorry” tace kanta a sunkuye. “Sorry? Meaning bakida ko paper knan?” “Yes” ta amsa sa. “Bakisan yau zaki fara min aiki bane da barakizo da shiri ba?” Farar jakarta side bag dake rataye kan shoulder’n ta Anas yasa hannu ya finciko, karap ta kama “Sir excuse me meh zaka min da jaka?” “Ki sake nace.” Yana ja tana ja “tunda bakida pape, rubuta details d’in zanyi akan jakan naki gobe baraki manta ki taho da paper ko jotter ba.” “Haba Sir taya zaka min rubutu a jikin jaka?” “Haka kikace?” Wayar ya mak’ala a kunnensa tare da tarewa da kafad’arsa kafin ta fahimci me ya ke shirin yi kawai taji yaja hannunta ya bud’o tafin hannunta tare da ciro biro daga aljihun suit nasa. “Yes David ina jinka, tell me the details.” “Mr. Fauzi me haka? Ka sake min hannu!” K’ok’arin fisgan hannunta take amman takasa dan yadda ya rik’e gamgam kafin ta sake wata maganar har ya fara mata rubutu kan tafin hannu. Hawaye take taji yana ciko mata a ido da k’yar tasamu ta shanye kukan dan nasihan da Mami ta mata jiya na tadena yawan zubda hawayenta gabansa. Hannunta ya mayar kamar paper harda yin cancelation, kallonsa ta tsaya yi sanda ya gama sannan taja hannunta a hankali. “In kika kuskura kika bari ya goge you’ll answer to me.” Sanin santsin hannunta nan da ‘yan mintuna rubutun ze gushe tashiga damuwan Anas again kawai tafito da wayar ta daga jakarta tayi copying duka details d’in ciki. Yana kallonta bece mata komi ba can data gama yace, “Allah sa wannan abin da kike kira waya yayi saving details d’in da kyau in bahaka ba you’ll get it from me.” Bata tanka sa ba ta mayar da wayar cikin jaka ta sake duk’unk’una kanta cikin hijabinta dan sanyi tana kallon window. A haka har suka isa destination nasu, nan take tafito daga motar bayan driver ya bud’e wa Anas yafito shima tabi bayansa tafiya take kanta a k’asa duk inda suka shiga gaishe da Anas ake. Chan sama suka haura zuwa wani hall manyan mutane ne ciki tas kowa da suit. A kujerar tsakiya Anas ya zauna take kowa ya gaishesa ita haushi ma mutanen suke bata gashi de almost dukansu sun girme Anas amman wai suna gaishesa ai ba laifin sa bane baya mutunta d’an Adam jibi yadda ya mayar mata da hannu kamar takarda d’azu, tsuka taja wanda bata san sanda yafito fili ba aiko tuni hall d’in ya d’auka kowa ya juya yana kallonta cike da mamaki harda shi Anas d’in. “I’m sorry please” yace da mutanen wajen “excuse us please.” Nan ya mik’e kafin Fannah tayi tunanin wani abu kawai ya fisge hannun ta yaja be tsaya ko ina ba se a bakin k’ofa. “What ia your problem? Meke damunki da zaki ja tsaki haka? Kinsan ko suwaye wad’ancan mutanen kuwa dazaki ja tsaki gabansu?” “I’m sorry” tace kanta a k’asa. Kallo ya bita dashi sama zuwa k’asa. “You better be, maza mu koma ki basu hak’uri.” Neck tie nasa ya giara ya shige ciki tana biye dashi a baya. Bayan sun shiga tabawa mutanen hak’uri duk suka giad’a kai da nufin sun hak’ura. Daman tsaye take kusa da Anas gudun kar ta sake masa abin kunya ya nuna mata kujera chan k’arshen hall d’in taje ta zauna. Tayi zaman zama gashi ba abinyi, bacci kawai ta mik’e kan kujeran tanayi har aka k’are meeting d’in bata sani ba. Anas ne yazo k’arshen fita chan ya hangeta tana bacci tsuka yaja sannan ya nufa kanta ya tsaya chan ya tsuguna daidai fuskarta tare da k’ure mata ido bacci take a hankali ba alaman tashin hankali tattare da ita, tayi pillow da hannunta ta hanyan aza kanta kan hannayenta biyu. Kallonta yake kusan na minti biyu, chan kad’an daga cikin hijabinta ya fad’o kan fuskarta hannu ya mik’a ze giara aiko daidai lokacin ta tashi a razane taja da baya ganin Anas a gabanta meyake shirin mata? Ina sauran mutanen sukaje? Kunya sosai Anas yaji, yanzu setace kallon ta yake ta raina sa. Ni Miemie nace daman me kake? “Gomma da kika tashi, da nasa an kawo min ruwa na watsa miki. Ni bansan wace erin lazy PA ce keba, daga zuwa meeting se bacci. Bakisan ya kamata duk abinda akeyi kema kisa kunnen ki kina saurara ba? This should be the last time.” Sauraransa kawai take amman d’an baccin datayin nan ya mugun sa mata yunwa. “Lets go” yace da ita nan ta mik’e tare da bin bayan sa. Kamar d’azu haka driver ya bud’e mota bayan ta shiga shima ya shiga. Akan suyi hanyan office nasu seta ga driver yabi wani hanyan daban. Rabin zuciyarta tana ce mata ta tambayesa ina zasuje, rabin zuciyar kuwa na hanata dan ko ta tambayesa ba amsata zeyi ba, banda ya gasa mata magana. Shiru tayi tana ganin ikon Allah. Chan gaban wani makeken hotel taga driver yayi parking k’arfin bugun zuciyarta taji ya k’aru meze mata a hotel? Innalillahi nan tashiga tsoro kasa rik’ewa tayi ta tambayesa. “Sir please me zamuyi anan?” “Abinda zuciyarki ke saka miki.” ya bata takaicaccen amsa. Wani irin tsoro taji ya sake rufeta. “Sir dan Allah kayi hak’uri.” “What a dirty mind dake, me da kike tunani zamuyi anan? A tunanin ki d’aki zan kama mana? LOL inma zan kama d’aki nan bada yara kaman ki ba. Abinci nazo chi in kinajin yunwa kuma lets go.” Shiru tayi bata basa amsa ba, ji take kamar ta nitse k’asa dan kunya mesa hankalin ta yaje da nesa haka? Abinci yazo ci bawani abu ba ta tunatar da kanta. Tana kallonsa har ya fice daga motar zuwa hotel d’in. Yunwa takeji amman barata ci abinci dashi ba, amman kuma batasan k’arfe nawa ze turata gida ba shida bakinsa yace mata in aiki yayi yawa ze rik’eta fiye da k’arfe 4:00PM. Wayarta ta ciro dan duban time k’arfe 12:30AM taga wai lalle sun sha awowi suna meeting kam. A hankali tafito daga motar zuwa cikin hotel d’in. Ba kowa wajen cin abincin da alama yayi reserving ne. A kujeran dungu ta hangesa da wayansa a hannu da alama jiran order’n sa yake. Har yanzu beyi noticing nata ba se sanda wani security yashigo “Miss kiyi hak’uri please anyi reserving wajen nan, nanda ‘yan mintuna meshi ze tafi seki dawo.” “I’m sorry” tace masa, a sanyaye ta juya zata koma cikin mota Anas ya danna mata kira “Miss Aleeyu.” Chak ta tsaya ba tare da ta juyo ba “security let her in.” “Miss Aleeyu Mr. Fauzi yace a barki ki shiga yana kiran ki.” Idanunta gam ta rufe rabin zuciyarta na ce mata tace wa security’n zata tafi rabi nace mata taje kiran Mr. Fauzi chan tabi zuciyar data ce mata ta koma cikin motan. Taku d’aya ta k’ara ya sake kiran sunanta “Miss Aleeyu!” wannan karan a tsawace b’ari ta soma wai mesa bare na kiran ta da sunanta ba se dana Babanta. A hankali ta juya k’afafunta suna rawa kanta sunkuye a k’asa, sejin idanunsa take a kanta, ignoring kawai tayi ta k’ariso gaban sa. Bata ce komi ba “sit” yace mata. Baki na b’ari tace, “Ss... Sir zan koma mota.” “I said sit!” Ya daka mata tsawa. Bata san sanda taja kujerar dake kallonsa ba ta zauna hannu ya d’aga waiter’n ya iso “make the plates two.” yace masa. “Okay Sir!” Tun bayan tafiyan waiter’n suka soma zaman kurame Anas kam se faman latse latse yake a waya. Bayan kamar minti uku abincinsu ya iso aka ajiye wa Anas nasa sannan itama aka ajiye mata nata. Ita kajin kai ne ma yamugun tsorata ta, batada kud’in biyan wannan plate dududu da dubu d’aya ta fito da, gashi already ta kashe d’ari biyu a zuwa kamar yadda zata kashe d’ari biyu a komawa d’ari shida ne kawai ze rage mata wanda tasan ba siya mata plate na gabantan zeyi ba. “Uhm please plate d’innan nawa?” Ta tambayi waiter’n. “N1,500 ne Miss.” Ya amsata a takaice yana murmushi. Miyau ta had’iye tare da waro idanunta dariya sosai tabawa Anas wanda da k’yar ya danne tare da yin tarin k’arya sarai ta gane da ita yake. Tace a mayar da plate d’in kuma tsoro take ji chan ta tuna zata je ta tambayi driver’n Mr. Fauzi cikon kud’in yaso ko gobe seta maido masa. Bayan waiter’n ya tafi ta mik’e tare da d’aga plate nata da nufin zuwa wani table. Blue eyes nasa ya d’ago yana kallonta. “Ina kuma zakije?” Kanta a sunkuye tace, “d’aya daga cikin tables d’in.” “Wannan kuma meya samesa?” “Babu kawai nag-” bata k’are maganar ba ya katse ta “sit.” “But Sir-” nan ma ya kuma katse ta “I said sit!” yafad’a a tsawace. Carap ta zauna tama kasa ko kallon abincin nata se yatsun ta da take murzawa wanda suka had’a gumi. Bayan yaja plate nasa gabansa ya d’au spoon “eat!” yace mata. Kai ta d’ago a hankali tana kallonsa shima kallon nata yake “ko cin abincin ne baki iya ba in kira d’aya daga cikin waitresses su baki?” “A’a na iya” tace tare da sunkiyar da kanta tana kallon abincin dakuma kajin da suke mata salamu alaikum! “Good, then eat nanda 20 minutes zanbar nan kuma ba jiranki zanba” yana kaiwa nan ya ajiye wayarsa yasoma cin abincinsa hankali kwance yakai kusan spoons biyar Fannah bata ko tab’a plate nata ba. Gugugur! Cikinta yayi k’ara sakamakon hakan yasa Anas dariya sosai amman seya danne yayi tari kad’an. Kunya taji sosai kamar ta nitse k’asa. A hankali ta d’au spoon d’in duk Anas na kallonta ta gefen ido. Da k’yar ta iya takai spoon d’aya baki sosai abincin ya mata dad’i, da kad’an kad’an tasamu tana cin abincin saboda yadda Anas yayi kamar besan tana zaune ba, abincinsa yake taci be sake kallon ta ba. Ko daya gama be motsa ba, bakinsa ya goge ya d’au wayarsa yana latsawa da wayo yake satan kallonta. Fannah kam ta baje se cin abincinta take, dam ta cika bakinta da fried rice d’in guda gudan salad cream d’in yamata staining baki kunya sosai taji da suka had’a ido da Anas. Take ta ajiye spoon d’in da k’yar ta had’iye abincin bakin nata sannan ta kora da ruwa ta goge bakinta bece mata komi ba yakira waiter’n, ganin haka Fannah tace, “sir excuse me please.” Har ta tashi Anas yace, “ba se kinje aran kud’i wajen driver ba I’ll pay for it” kunya sosai taji wai ya ma akayi yasan abinda takeson yi kenan? Wannan Mr. Fauzi se Allah. Cike da kunya da k’yar tace, “thank you.” *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:50, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 5⃣0⃣ Kamar wanda bareyi magana ba yace, “naji tashi mu tafi.” “Promise me baraka kira boss nasa ayi firing nashi ba.” “Thats none of your business, he deserves to be fired.” “Please Anas for me, please karka kira Boss nasa kaji Anas? Please.” “Fannah no!” Ya fad’a ad’an tsawace. Fuska ta maraice, “Shikenan tunda d’an wannan ma baraka iya min ba” jakarta ta tattara ta mik’e da niyyan tafiya gyalenta ya rik’o. Da k’yar bakinsa ya iya furta “no don’t go, barin kira Boss nasan ba, just don’t go.” Dad’i taji sosai da murmushi ta juyo tana kallonsa “thank you, so ka hak’ura muci abincin anan?” “No not here, lets go somwhere” be jira tace wani abu ba yakama hannunta suka fice, gidan baya suka shiga dukansu a yayinda driver ya kunna mota. Ita yanzu Fannah damuwarta d’aya ne yadda zata masa wa’azi yadena rik’e mata hannu, tana son tabisa a hankali ne kar ta had’a masa komai lokaci d’aya shiryuwan ma yace yafasa akoma gidan jiya. Gaban wani makeken hotel driver’n ya tsaya bayan ya bud’e musu k’ofa Anas yafito sannan ita, ciki suka shiga hannunta rik’e cikin nasa sede yau da mutane cikin hotel d’in zaune suna cin abinci ana ganinsu aka soma gulma k’us-k’us. Magana take iya yadda Anas ne ze jiyota. “Anas kad’an sake min hannu kaga duk maganan mu suke kaji please.” Banza yayi da ita ya nufa wajen receptionist. “I want to reserve this place now.” “Okay sir bara a sake karb’an customer ba, but bari na cikin su gama please.” “Kasan ko waye ni? I said reserve it now ka koresu duka I will pay you double of the money.” Ido ya zaro sosai jin double, “okay sir, bari amusu magana.” Haka mutanen suna ji suna gani aka kaisu wani d’an waje suka k’are cin abincin chan, aka barwa Fannah da Anas kad’ai makeken wajen. Kujeran tsakiya suka zauna ya musu ordering abincin, bayan minti uku abincin nasu ya iso spoon nasa ya d’aga ya soma ci, yayi spoons biyar yaga ko tab’a nata batayi ba. “Fannah why are you not eating? Acanzo miki ne?” Kai ta girgiza “Anas dole in zakaci abinci sekayi reserving ne?” “Yes wani abu ne?” ya tambayeta yana cin abincin sa. “No-” kafin ta k’ara fad’in wani abu yace, “banasan surutu while eating just keep quiet and eat okay?” Kai ta giad’a masa ta soma ci a hankali, kamar kullum yagama yayi zaman jirarta, wayarsa dake ringing ya d’aga “okay then” yace tare da katsewa. Bayan tagama ci ya biya suka fice gidan gaba ya bud’e mata cike da mamaki tace, “Anas ina driver’n yaje?” “He went somewhere, I’ll be the one to drive, enter.” “Sir zan tafi da kaina” haka kawai taji batason tana shiga mota dashi kad’ai. “Miss Aleeyu kina b’ata min lokaci zanje masjid get in.” Zata sake magana yace, “now” a tsawace. Ta tsorata amman ta dake “sir ni zan tafi da kaina.” “I’m your boyfriend ko kin manta? Kishiga ko in d’aga ki in saki ciki da kaina.” Miyau ta had’iye tashiga a hankali danko tasan Anas baida kunya tsab ze d’agata. Nan ya rufo k’ofar, not long enough yatada motar, agogon hannunsa ya duba yaga 15 mins to 12:55PM lokacin sallan juma’ah. “Fannah” ya kira sunanta, nan tabar kallon windown da takeyi ta juyo dad’i sosai yake mata yadda Anas ke kiran sunanta ‘Fannah’ cikin daddad’an muryarsa, har setaji ta sake k’aunar sunan nata inama dashi yake kirarta kullum. “Yes” ta amsa sa. “Can you wait in idar da sallan juma’ah se in kaiki gidah?” Kai ta giad’a masa daga nan be sake cewa komai ba a inda manyan mutane suke parking motocinsu yayi parking nasa a space da aka tanada masa, a kunne yabar motar dan AC’n daya kunna mata. “I’ll be right back.” “Okay” tace masa tana kallonsa har ya b’ace cikin mutane, shiru ta zauna tana d’an kalle kallenta chan bacci ya d’auketa wanda batasan yaushe ba. Bayan 25 ninutes Anas ya dawo yana bud’e motar yaga Fannah na bacci da wuyanta karkace gefe d’aya, gyalenta kuwa rabinsa ba’a jikinta yake ba hakan yabawa Anas daman k’are wa k’irjinta kallo, yayi kusan minti d’aya yana kallonta sannan take ya kawar da kansa yana girgizawa “no this is not approppriate.” Zagayowa yayi ta side nata ya kwantar mata da kujeran yadda zatafi jin dad’i tare da gyara mata kanta agarin haka d’ankwalinta ya kunce. “Oh no!” Anas ya fad’i k’asa k’asa. Allah yaso ribbon natan be kunce ba, yanayin gashin dake kwance kan goshinta da sajenta ya tsaya yana kallo, besan sanda ya d’aga hannunsa ya shafa kan sajen fuskartan ba, ganin ta d’an motsa yaja hannun nasa baya da sauri gudun kar ya farkar da ita. Mayafinta yaja a hankali ya rufe mata k’irjinta dashi, kanta kuwa d’ankwalin ta ya bud’a ya d’an rufe mata gashinta sama-sama sannan ya rufo k’ofar yadda bareyi k’ara ba. Side nasa ya nufa ya shiga ya zauna sede sam ya kasa kunna motan a gudunsa kar ya fara driving kuma ta tashi in suka d’an hau kan bomb. Zama yayi tare da ciro wayarsa yana chatting yana zaman jiran tashin Fannah. Bacci sosai takeyi chan ya juyo yana kallonta, kallo na sosai, cameran wayarsa yashiga yayi positioning sannan ya d’auketa picture d’aya, ganin tayi kyau ya k’ara mata d’aya kasa hak’ura yayi seda ya mata pictures kusan hamsin har anan bata tashi ba. Gallery ya shiga yana ganinsu one by one ko d’aya ya kasa deleting cikin hamsin da biyun duk ba wanda be masa ba. Awa biyu Fannah ta d’au tana bacci se 3:00PM ta tashi sam Anas yak’i tada ita meetings guda biyu dayake dashi, Kacallah yakira dan tunasar dashi amman haka ya fasa zuwa dan yadda bayasan ya tada Fannah yace ayi rescheduling kawai. A hankali ta soma bud’e idanunta har tagama bud’e su fuskar Anas ta soma cin karo dashi sede ba ita yake kallo ba hankalinsa na kan wayarsa. Kanta ta tab’a taji d’ankwalin ya since, data kai dubanta kan jikinta kuwa taga an rufeta da mayafin ta wanda she is sure ba ita tayi ba, toh waya mata? Mr. Fauzi? Omg! Yanzu yaga k’irjina ta fad’a a azuci. Gyaran murya tayi wanda yadawo da attention nasa kanta. “Se yanzu kika ga daman tashi? You’ve been sleeping for about 3 hours.” “What?!” Tayi exclaiming tana kai dubanta wajen agogon motan taga 3:03PM “Ya Salam!! Banyi Sallah ba.” “Toh laifin waye? Shikenan mutum ba’a iya bar masa AC kunne seyayi bacci?” Kunya taji sosai ita kanta batasan sanda tayi bacci ba. “Kinsan meetings nawa nayi canceling saboda ke?” Kanta a sunkuye tace, “I’m sorry ai da ka ta dani.” “Ni ban iya ta da mutum in yana bacci ba, a banza kin samin ciwon kunne.” “Ciwon kunne kuma?” Ta tambayesa ba tare da ta kallesa ba. “Yes, da wannan minsharin da kika tayi.” Minsharin kuma? Ta nanata a ranta. Tunda take ba’a tab’a ce mata tana minshari ba se yau. “Sir but bana minshari ni fah.” “Awww maqaryaci kikeson kirana kenan?” Ya tambayeta tare da d’age gira. “A’a ni ba abinda nake nufi ba kenan.” “So bayan kin gama b’ata min precious time kin sa min ciwon kunne da maqaryaci zaki sak’a min?” “I’m sorry” tace ba tare da ta kallesa ba. Motar ya kunna suka soma tafiya har bakin k’ofar gidansu ya kaita, bayan ya sauk’e ta tamasa godiya “wait” yace mata. Gefen k’ofar sa yasa hannu yaciro littafin d’azu na «HALF BAD» data jima tana nema ya mik’a mata, kallonsa ta tsaya yi cike da mamaki. “Ungo amshi.” Bata san sanda ta soma murmushi ba “but sir-” katseta yayi “jeki karanta.” dad’i sosai taji wanda ta kasa b’oyewa “Thank you so much” tamasa godiya tare da ficewa, seda ya tabbata ta shiga gida ya juya shima yatafi. ***** _Washegari..._ K’arfe 8:00AM na safe Anas ya tashi da hoton Fannah yayi sallama danko yana tashi ya d’au wayarsa yakai kan pictures nata daya d’auka jiya. Yafi minti uku yana kallon pictures d’in sannan ya tashi ya nufa toilet bayan ‘yan mintuna ya fito shirin sa na kullum da safe yayi ¾ da vest all in black sannan yafita. Already yasamu kowa kan dining table bayan ya k’arasa ya zauna suka gaggaisa. Amal dake gefensa tace, “Ya Anas ni rabuwa da inyi game a wayarka harna mance.” “Angel duk game da nake dashi fa kema na miki installing.” “Ya Anas ni nafison yi anaka.” “Naji gashi” nan ya mik’a mata wayar. “Yeyy! Thank you.” “Wai Amal ke ana breakfast baraki ajiye wayan ba?” Cewar Ummie. “Ayyi mana Ummie.” “Ajiye wayan” Abuu ya fad’a ba wasa. “Se in kin gama breakfast naki kiyi.” Kamar wacce zatayi kuka tace, “Ya Anas kace musu su barni inyi.” “Toh da Ya Anas da Abuun waye babba?” Cewar Shettima “Abuu fad’uwa d’aya kawai zatayi seta karya ko Angel?” “Eh Ya Anas.” Nan ta buga d’ayan tana fad’i tace, “Ya Anas mu d’au selfie tunda duka munsa black clothes.” Ba musu yace, “okay” nan ta shiga snapchat ta d’aukesu, sosai sukayi kyau. Gallery ta koma tana zooming faces nasu mistakenly hannunta yayi gefe aiko hoton Fannah ya bayyana. “Ya Anas wannan ba hoton Fan-” bata k’are maganar ba yasa hannunsa ya rufe bakinta da sauri. “Shut up kinji?” Sanda ta gyad’a kai ya sake mata bakin. “Don’t tell anyone kinji Angel zan kaiki shopping anjima.” “Shopping kad’ai Ya Anas?” “Toh meh kikeso?” Duk wannan magana da suke su Abuu sun zura musu ido suna kallonsu. “Acanza min waya.” “Angel kap ajikinku masu iphone 6 nawa ne? Ai naki ne babba.” “Ni 6+ (plus) nakeso.” “Toh naji zan saya miki karki fad’awa kowa kinji.” Kai ta gyad’a masa. “Meh wannan abun da ba’aso a sanar damu”Abuu ya tambaya. “Babu” Anas ya basa takaicaccen amsa. “Ni zan fice se anjima” ya fad’i tare da d’aukan wayarsa. “Baba na ka fasa karyawan kenan?” Ummie ta tambaya. “Eh Ummie zanje inchi a waje.” Allah Allah Shettima yake su k’are breakfast yaje yabuga cikin Amal har seta fad’a masa abun. Bayan sun k’are yaje ya sameta kwance kan gado a d’akinta da ipad nata se temple run take bugawa. “Amal” ya kira sunanta alokacin daya zauna kan gadon nata ko noticing nasa batai ba dan yadda hankalinta yabi game d’in. “Ke Amal!” ya sake kiranta. “Meh?” ta fad’i tana cigaba da buga game nata. Ganin inba wai amsar ipad d’in yayi ba barata basa hankalinta ba yasa hannu ya k’wace. Kuka ta fashe masa da “wallahi Ya Shettima Allah ya isa nayi nisa fa ka kama ka k’wace kuma sena fad’awa Ya Anas. Kabani ipad d’ina.” “Da Allah mumu kawai kika san dawata magana nazo miki da?” “Banasan ji ni tunda garin Allah ya waye ban kula kaba, kabani Ipad d’ina ko in fad’awa Abuu.” “Haba Angel d’in Ya Anas ‘yar gaban goshi yi hka’uri kiji?” “Meh?” ta tambaya tana zumburo d’an bakinta. “Batun hoton da kika gani wayan Ya Anas ne d’azu nakeson ki d’an fad’amin kinji Amluuluu na, ‘yar autar mu guda.” “O’o ni barin fad’a ba, bani Ipad d’ina.” Hannunta yaja ta fad’a jikinsa take ta tashi tana mayar da gashinta baya. “My Amaluuluu tell me mana zan kai ki shopping.” Dariya ta b’arke da, “kaida ko ka kai mutum shopping befi ka siya masa chocolates guda biyar ba kace ya isa, banaso. Ya Anas yace ze siya min 6+.” “Ke dad’i na dake bakida wayo, yaushe Ya Anas ze siya miki 6+ wallahi k’arya yake miki, trust me.” Kafad’a ta buga da nufin o’o. “Fad’amin mana hoton waye ne?” “O’o barin fad’a ba, ai dama na fad’a maka wataran zakazo neman abu wajena. Barin fad’a ba ni kabani ipad d’ina.” “Mumu kawai karki fad’an, tayi tsami maji.” Nan yamata wulli da ipad d’in. “Ke dama ba’a harka dake mschww.” “Eh d’in mutum ace se gulma.” **** Anas ne zaune a paint house nasa har yanzu be karya ba pictures na Fannah kawai yake ta kallo, ganin ba mahalicci se Allah kawai ya danna mata kira, ringing d’aya biyu ta d’aga “hello Mr. Fauzi” kasancewar Afrah batta d’akin. “Fannah” yakira sunanta. “Na’am” ta amsa. “I’m hungry.” Toh nikuma nice me baka abinci tace a ranta. “Toh Mr. Fauzi me zan maka? Kaje kaci abinci mana.” “Not until nasha coffeen ki.” K’arya ta masa, “banida lafiya bareyi infito ba yau Mr. Fauzi.” Yanaji yagano k’arya take. “Toh shikenan, I’ll look for my beer insha kawai.” “A’a please karka sha.” “Then come.” Nisanta tayi chan tace, “okay, naji zanzo karka sha please kaji?” “Then kizo da wuri in bahaka ba zan sha.” “Mr. Fauzi promise me baraka sha ba please.” Shiru yayi bece komai ba “please...” “Okay.” Nan ya katse. Daman tayi wankanta, d’aya daga cikin had’ad’d’un abayoyin da Anas ya siya mata irin na ‘yan Sudan d’innan tasa. Rolling tayi had’ad’d’e me kyau gashin ta yamata acuci me kyau. Tana fitowa suka had’u dasu Mami tsakar gida suna aikin breakfast da Afrah bayan gaisuwa Mami ta tambayeta “ina zakije haka Fannah da wannan uban kwalya?” “Kai Mami jan baki fa kawai nasa ko in goge?” “A’a barsa ina zakije?” ”Mr- I mean Anas ne yake nema na zeyi introducing d’ina ma wasu business colleagues nasa.” “Aww hakane? Toh Allah kiyaye, Fannah banda yawon banza kinji? Ni na yaba tarbiyyan Anas ba irin ‘yan iskan mazan nan bane amman still ki kiyaye kinsan shi D’A NA MIJI DA SABON SALO yake, a kullum” (book na Lubiee finest!) “In shaa Allah Mami na tafi.” “Asha love lafiya, in an sai ice cream kuma a tuna damu” cewar Afrah. Banza da ita Fannah tayi tana fitowa ta tsari napep. In 25 minutes time ta iso paint house na Anas. Golden side bag nata ta daidaita sannan ta k’arisa, bell ta danna yana zaune a parlour ya taso ya bud’e mata. Kallonta yatsaya yi kamar ze cinye ta, sosai abayan ya karb’eta. “Kinyi kyau” yace da ita. Batasan lokacin da ta soma murmushi tana blushing ba. “Thank you” tace tana k’ok’arin kare fuskarta. Gefe ya matsa mata ta shiga, direct kitchen ta nufa ta had’a masa cikin flask biyu harda na gobe sannan ta juye saura cikin cup ta kai masa. “Sir zan koma.” “No girlfriend wait for me in gama se in kaiki.” “Karka damu I can manage.” “No girlfriend your boyfriend insists, kidena so kina kaiwa kasuwa kinji girlfriend?” “Ni kadena cemin girlfriend please, ai ba cikin mutane muke ba.” Killer smile nasa ya sakar mata sannan ya cigaba da shan coffeen sa yana gamawa ya d’au key’n sa “lets go ko girlfriend?” Ba gardama ta mik’e suka fita shi da kansa ya bud’e mata motar nan suka fice. Cool music ya kunna a motar. Fannah kuwa in akoi abinda ta tsana befi wak’a ba. “Anas” ta kira sunansa cikin siririyar muryarta. “Yes Fannah” ya dawo da kallansa a gareta yana tuk’i. “Nace will you mind turning off the music, please?” “Why?” Ya tambayeta. “Anas ba kyau.” “Mene ba kyau d’in?” “Jin wak’an.” Ta amsa sa. “Ke shikenan komai ba kyau, shaye shaye ba kyau, rik’e hannu ba kyau yanzu kuma jin wak’a ba kyau?” “Mr. Fauzi narkekken dalma ake sama duk me sauraren wak’a a kunne, is better ka kunna karatun Al~Qur’ani kana sauraro mala’ikun rahma suna sauk’a.” Shiru yayi bece komai ba. “Kaji Mr. Fauzi my boyfriend.” Kallonta ya juya yayi this is the first time take kiransa her boyfriend seyaji kawai yanasan ya fasa jin wak’a ma gabad’aya. “Zaka dena?” Ta sake tambayar sa nanma bece komai ba. “Please Anas, for me, please kaji?” Kai ya gyad’a mata. “Sir say yes please.” Nisanta yayi “yes zan dena.” “Yeyy! Mr. Fauzi thank you, now promise me daga yau baraka sake jin wak’a ba.” “I promise”. Ya amsa ta a takaice nan ya ciro CD d’in yayi wulli dashi waje. “Zan siyo qira’a gobe ko anjima.” “Yawwa Mr. Fauzi, thank you so much.” Daidai lokacin Kacallah ya soma kiransa bayan ya d’aga Kacallah ya masa wasu bayanau. “Okay bari zanje gida yanzu in duba I think yana d’akina okay. Will call you back.” “Fannah” ya kira sunanta yadda takeso. “Na’am” ta amsa tare da juyawa. “I suppose to take you home amman I need to get something daga gida it won’t take long kin yarda?” “Yes ba komai” ta amsa sa. Gaba da gidansu kad’an yayi parking. “I’ll be right back, don’t leave this car kinji ba? Karki shiga cikin gidanmu, am I clear?” Kallonsa take cike da mamaki shikuma rowan gidansu yake? mschww, thank god ba ita tace ya kawo ta ba. K’in amsa sa tayi. “Fannah Aleeyu am serious karki shigo ni na fad’a miki” yana kaiwa nan ya fice sekuma ya sake dawowa ya kashe AC’n “kafin ki sake min bacci a mota.” Harara ta watsa masa ganin bai kallonta had’ad’d’en gidan dake layin taga ya shiga. “Mschwww sekayi ai.” Wayarta ta ciro ta cigaba da buga candy crush nata. Bayan minti biyar shiru Mr. Fauzi befito ba har yanzu kaman ance ta d’aga kai ta hango dawakai guda biyu sun fafaro da gudu mutanen kansun ma sun kasa controlling, “wayyo Allah doki! Nashiga uku!” Fannah uwar tsoro ai bata san lokacin da ta fita daga motar ba a 360 bata fad’a ko ina ba se gidansu Anas. *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:50, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 4⃣9⃣ Kallonta yake kamar TV a yayinda take sauri sauri tayi tagama dan zuwa samin Yusuf. Guda 4 tayi cikin goma amman wani zogi hannunta ke mata saboda tsawon mails d’in, idanunta ta d’ago tareda maraice fuska koze d’an ji k’anta. Sosai shima yaji ta basa tausayi amman kuma ya ya iya? In yace tabari definately zata je ta samu Yusuf abinda baiso kenan, shikuma bayasan raini bayasan tasan kishinta yake ta d’au ko sonta yake (ni Miemie nace toh da ba sontan kake ba?) Yanason ce mata barata fita da Yusuf ba amman bayasan ta d’auka da wani manufa ta d’au ko santa yake kanta ya soma girma. Kansa ya kawar daga gareta kawai dan kar tausayinta ya kama sa tare da concerntrating akan laptop nasa. Bayan tasamu tayi guda takwas ta d’ago kai “Mr. Fauzi please kayi hak’uri nagaji.” Banza da ita yayi. “Mr. Fauzi please” nanma bece da ita komi ba dan yasan muddin bakinsa ya bud’u zece ta ajiye shikenan, abinda baiya so kenan. Wayarta ne ya soma ringing tana kai dubanta taga Yusuf ke kira bayan ta d’aga tace, “Yusuf I’m sorry wallahi aiki ne yad’an rik’eni amman I’m almost done yanzu zan sauk’o.” Nan ta katse. Anas dake sauraronta yace a ransa yanzu zaki sauk’o ba? We shall see. Bayan 10 minutes tagama, wani hamdala ta saki se murza yatsunta take dan azaba. “Sir gashi na gama” ta sanardashi alokacin da take tsaye gaban table nasa. Amsa yayi yana dubawa one-by-one komai yayi sede bayasan ya barta ta tafi, taya zataje tayi having lunch da Yusuf bayan gashinan, bayan tasan tare suke ci always, Isn’t he her boyfriend? Ai koda relationship nasun na k’arya ne still be kamata ba. Besan meh ba amman yanzu bayasan ganin Fannah da wani d’a na miji in ba shiba. “Sir can I go now?” “Wait” yace, tare da zaro d’aya daga cikin papers d’in “seda nace miki be careful banason cancelation kalli nan. D’au new plane sheet ki sake copying.” Kamar wacce zatayi kuka tace, “ayyaahh manaaaa Sir mana, letter ‘f’ nefa kawai nayi canceling its not looking rough ai.” “Ma ke kenan, to me it is morethan rough...” Yacigaba da duban sauran nan ya tsakula wasu guda ukun da tad’anyi light mistakes, in aka had’a dana farkon hud’u kenan. “Recopy them all duk kinyi omiting mistakes” Baki ta sake, “Mr. Fauzi wallahi barin iya ba dan Allah karka min haka.” “Miss Aleeyu what is wrong with you? I am paying you bawai aiki kike min kyauta ba d’auka kije ki zauna ki gama yanzu.” Ya fad’i authoritatively tare da kawar da kallonsa daga gareta. Harara mai rai da lafiya ta watsa masa ganin bai ganinta sannan ta tattara ta koma ta zauna. Yusuf takira ta basa hak’uri kan fitarsu bareyi ba seko next week saboda tasan ba yanzu zata gama ba, hannunta yayi tsami layi d’aya ta rubuta seta tsaya taja yatsunta. “Ba komai” yace “Allah kaimu” tare da katsewa. Dad’i sosai Anas yaji dayaji tace ta hak’ura. Kallonta yake tayi ta tsaya tayi ta tsaya tana gama guda d’aya tausayinta ya kama sa, tasowa yayi daga kujeran sa ya nufo gabanta, ita a zatonta ko yaga mistake na ‘a’ da ‘e’ da tayi ne yazo mata masifa. A maraice tace, “Sir dan Allah kayi hak’uri don’t make me recopy it please, wallahi guda d’aya ne kuma bara’a gane ba” ta k’are maganar kamar wacce zatayi kuka. Tsugunawa yayi a gabanta, ido wuru-wuru ta zaro meyake shirin yi? Kafin ta kawo wani abu a ranta ya ja hannunta a hankali, bugun zuciyarta taji ya k’aru, a hankali take k’ok’arin k’watan hannun nata gudun karya k’ara mata wasu papers d’in. Biron ya amsa ya ajiye tare da bud’o tafin hannunta me uban laushi yana mata tausa a hankali daga kan yatsunta har zuwa wrist nata. Har wani sanyi sanyi takeji saboda yadda hannun yayi tsami yana mata ciwo amman kuma be kamata tabar masa hannunta yana tab’awa harda mata tausa ba. “Ermmm Mr. Fauzi” ta fad’i tana k’ok’arin karb’e hannun nata, sarai yagane tanason k’watan hannunta ne amman be kula ta ba, hasali yi ma yayi kamar be san tanayi ba, sanda ya tabbata ya mata tausan da yaci ace hannun ya bar zafi ya bari. Mik’ewa yayi ya koma ya zauna ba tare da yace da ita komi ba, dukda kuwa so yake ya bata hak’uri amman inaaa girman kai! Bayan ya zauna ta d’aga biron daga inda ya ajiye da nufin cigaba da rubutun tunda ba cewa yayi ta bari ba. Bece komi ba har yanzu se da yaga zata fara rubutun. “Keep the pen, stop it, don’t write.” Ya bata wannan commands. Kallonsa take fuskarta d’auke da kan mamaki. “Sir bangama bafa-” “I know” ya katse ta, “just kibari don’t write again.” Dad’i sosai taji yanzu seta samu tafita da Yusuf ma tunda Boss yace tabari. Arranging papers d’in tayi ta kai ta ajiye masa kan table sannan ta koma ta d’au jakarta ta saqala, duk kallonta yake bece komai ba seda ta kai bakin k’ofa ya daka mata kira “Miss Aleeyu!” Har tsakiyar kanta tajiwo muryarsa. Juyowa tayi tana b’ari dan firgitan da tayi. Toh me tayi kuma yanzu? Da hannu yayi gesturing nata kan tazo. Taku take k’afa na rawa har takai gaban table nasa. “Who asked you to leave?” Ya tambayeta yana kallon cikin idanunta. Da sauri ta kawar da kallonta elsewhere ba tare da tace komai ba. “Am talking to you!” ya fad’a ad’an tsawace duk ransa yabi ya b’aci har yanzu be yarda Yusuf nada gut daze ce zekai Fannah cin abinci ba, yaushe ma yagama ciyar da kansa kuma awani local restaurant zekaita ko hotel ma bare iya kama musu ba to talk more of ya musu reserving. I’ina tasoma “ermm.. Si.. Sis.. Sir naji kace in ajiye in bari kuma aikin daka sani kenan.” “Amman nace ki tafi?” Kai ta girgiza a hankali. “Good kinga book shelve d’in can?” Kai ta giad’a tana kallon shelve d’in. “Jeki min arranging nasu.” Kallon shelve d’in ta tsaya yi nakusan ‘yan mintuna sannan back to Mr. Fauzi. Itade bata ga abin gyara cikin shelve d’in ba ga books nan duk anyi arranging nasu tsatsaf. “Bakiji me nace bane?” Ya tambayeta. “Naji Sir amman kuma naga ba abin gyara ciki, shelve d’in is well arranged.” “Toh ni banasan arrangement d’in na hannun dama a k’asa nakeson su koma hannun hagu a sama. Na tsakiya ki dawo dasu second to the last row, second row ki raba into two a 4th raw...” Haka ya ringa juye-juye. Kallonsa take kamar tayi kuka, ita ba abinda taji ma inbanda na hanun dama a k’asa su koma hannun hagu a sama. “Well baraki fara bane?” “Zan fara” ta amsa sa a takaice murya k’asa k’asa. Jakarta ta ajiye ta nufa wajen book shelve d’in. A hankali ta fiddo da na saman tayi replacing nasu dana k’asan kamar yadda ya buk’ata, a yayinda shikuma ya katse duk wani abinda yakeyi yana kallonta ko kyafta ido baiyi. Itade Fannah arranging take yadda taga dama, chan ta tsaya admiring wani latest english novel data jima tana nema bata samu ba. «Half Bad by Sally Green» kusan na minti biyu tana kallon littafin sannan ta had’a da sauran ta cigaba. A takaice de seda ta kusan awa tagama had’a uban book shelve na Anas dake nan kamar library. Daidai lokacin k’arfe 11:30AM kenan. Tagaji iya gajiya. “Sir na gama” tace all exhausted, ga wani uban yunwan daya keto mata lokaci guda. Bece da ita komai ba illa d’akinsa da ya nufa bayan like 5 minutes ya fito se k’amshin turare yake, gashin kansa ma ya sake gyarawa, kallonsa Fannah ta tsaya yi. “My girlfriend” yace da ita yana kallonta dawani killer smile tattare da fuskarsa shikansa yasan yayi kyau yau. Zuciyarta taji ya tsallaka bugu uku lokaci guda, kai ta d’ago a rikice tana kallonsa da ita yake koko a’a. “Me?” Ta tambayesa tana nuna kanta. “Yes you, you are my girlfriend ko kin manta ne?” Lallai ma! Kallansa take cike da mamaki yanzu yagama azabar tar da ita yawani zo yana shegen murmushinsa yana kiranta girlfriend nasa. “I’m hungry muje muci abinci nasan kema you must be hungry.” Yunwan takeji amman ta dake “no I’m not ni barinje ba kawai ka sallameni in koma gida.” “No ba gidan da zakije, we are going to eat, oya stand up na baki 5 minutes kije ki kimtsa a office naki.” Yi tayi kamar bata ji saba. “Miss Aleeyu! Don’t try my patience.” Ganin bai kallonta ta galla masa harara kan zata cire idanta sannan ta mik’e tare da jan jakarta ta fice zuwa office nata wajen book shelve d’in ya nufa yad’anyi dube-dubensa. Exactly after 5 minutes d’in yafito daga office nasan itama a daidai lokacin ta fito. Light makeup nata ta gyara ta hanyan k’ara powder da zalla datayi sekuma d’aurinta data sake gyarashi. Gyalen nanan yadda yake d’azu ta yafasa kamar yadda Afrah tamata d’azu. Kallonta yake wane ze had’iyeta. A hankali cikin k’asaita ya tako gabanta gam ta rufe idanta tana jiran ya fara suburbud’a mata surutu setaji ya kama hannunta take ta bud’e idan so take tace masa ya sake mata hannu sekuma ta tuna there will be no point doing so dan ba jin maganarta zeyi ba. Wajen elevator’nsa suka nufa bayan daya bud’u tace, “Sir semun nunawa duka ‘yan office naka muna dating ne? Kabari in mun fita anan amnan yanzu ka sakemin hannu please.” Ko tanka ta beyi ba illa janta waje da yayi suka soma tafiya. Take floor d’in yakama da surutu da gulma kowa se tofa albarkacin bakinsa yake k’us-k’us dan sun san halin Boss yanzu seya buga fire! Kunya ne ya rufe Fannah kamar ta nitse k’asa yanzu shikenan zasuce daman abinda ita da Mr. Fauzi keyi kenan kullum a office nasa, soyayya. Da idansu ya had’u da receptionist kuwa harara ta watsa mata dan ta jima da fad’awa tarkon san Mr. Fauzi koda ta fad’a masa kuwa tatas ya mata ya k’yamace ta. Ignoring nata kawai Fannah tayi, Yusuf dake shigowa yanzu ne yagansu tare da Mr. Fauzi amman ko kad’an idanunsa be kai kan hannun su ba. “Fannah!” Ya danna mata kira a yayinda ya gama k’arisowa kusa dasu. “About the lunch I think zamu-” be k’are maganar ba idansa ya sauk’a kan hannun ta dana Boss. Ido wuru-wuru ya zaro sekace a mafarki! Me had’in Fannah da Boss to kodai soyayya sukeyi? Fannah da hanaklinta zatayi soayayya da me shaye shaye? “Oh I’m sorry bansani bane daban gayyaceki lunch d’inba” ya fad’a tare da juyawa. Fannah ji take kamar ta nitse k’asa. “Yusuf” Mr. Fauzi ya kira sunan sa chak ya tsaya tare da kewayo wa. “ *SWEETHEART* baki sanar dashi bane dama? Why?” Shiru tayi bata amsa saba. “Tell him now to clear all doubts.” Nan ma bata tanka saba. Hannunta dake cikin nasa ya matse yadda ze d’an mata zafi. “Na zata na fad’a masa, Yusuf I’m sorry.” “Sorry for what? Don’t apologise *HONEY* fad’a mashi yanzu.” Shiru tayi duk takaici yabi ya cikata. “ *QUEEN*,ko yunwan ne bakiya son magana? I’m sorry yanzu zamuje muci abincin just tell him kinji *HONEY BOO?* ” Wai meke damun Mr. Fauzi ne ta tambayi kanta so yake yayi ruining friendship nata da Yusuf ne ko me? In yacigaba da abinda yakeyi ai se Yusuf ya d’au k’arya ta masa d’azu batun aikin dayace ya mata yawa, se yace ko k’arya ta masa daman fita zatayi da Mr. Fauzi take b’oye masa. Ido kawai ta rufe tace, “Yusuf I’m sorry ban fad’a maka ba, Anas is now my boyfriend excuse us please zamuje muchi abinci.” Mamaki ne sosai ya ratsa Yusuf lallai ma Fannah tacika ‘yar halak. “I’m sorry for delaying you, by the way congratulations” a sanyaye ya juya yayi tafiyarsa, binsa da kallo Fannah tayi, ji take kamar tayi kuka, mesa Mr. Fauzi ze mata haka? Bata sake ce masa komai ba har suka isa hotel d’in shi da kansa ya bud’e mata k’ofa se dad’i yakeji saboda yasan definately yanzu Yusuf da yake zaton saurayinta ne ze rabu da ita tunda ya gansu tare. Abinci kala d’aya ya musu ordering kafin abicin ya iso ba abinda Anas yake inbanda kallon Fannah shi inama haka zata namasa shiri kullum. Duk lokacin data d’aga kai setaga ita yake kallo. Da k’yar kalamun dayakeson kiranta dasu tun d’azu da safe suka fito yanzu, “you are looking beautiful today.” Kai ta d’ago tana kallonsa da mamaki karara a fuskarta. Wayace mata tayi kyau? Mr. Fauzi? Kode k’arya kunnuwanta suke mata. “Eh sir?” Ta tambayesa. “Not Sir, Anas” yayi warning nata. “Anas me kace?” “Nace kinyi kyau yau.” Ido wuru-wuru ta zaro yau wata rana Mr. Fauzi ya yabata, sede bata san meh ba seta tsinci kanta cikin jin dad’i, toh se meh dan yace tayi kyau? Se komai ya faru k’wak’walwarta ta bata amsa. Murmushin jin dad’in datayi k’ok’arin kawar dashi ne ya kub’uta mata, kallon ta Anas yake dad’i yaji yasata murmushi. “Thank you” tace a hankali cikin jin dad’i, take ta nemi bak’in cikin daya tusa mata ta rasa. “You too kayi kyau.” “I know already ba sekin fad’a min ba, I always look good.” Toohhhh! Ta d’ago kai tana kallonsa yaga shima ita yake kallo, shegen girman kai tace a zuciyarta wai I always look good irin yasan shi kyakkyawan nan ne, Allah raba mutum da erin wanga hali. “My girlfriend nasan ban isa in hanaki kallo na ba amman kallon yayi yawa unless you wanna eat me up.” Wai lallai ma tace a ranta wato shi ya zage yana kallona in ni nad’an kallesa yace wani na cika kallo. “But Sir naga nima ai kallo na kake, kuma tun d’azu tunda nashigo office naka yau.” “Toh ai dan na kalleki doesn’t mean anything, ni kawai kallon ki nake saboda kin d’an yi kyau yau kuma ni bada wata manufa nake kallonki ba amman kinga ke kullum cikin kallona kike, day and night kuma da wata manufa kike kallo na. I can see it in your eyes, kallon soyayya kike min nikuma nayi warning naki don’t fall for me.” Bakin Fannah seda ya kusa fad’i a k’asa dan yadda ta sakosa. “Nide ba kallon soyayya nake maka ba.” Ta fad’a tare da kare kanta. “Ohonki nide na fad’a miki *SWEETHEART* don’t fall for me.” Dadai lokacin abincinsu ya iso. Waiter’n ranan ne ya kawo musu wanda ta tambayesa nawa ne kud’in plate. “Wow Miss Aleeyu you are looking amazing.”,Murmushin daya k’ayata ta tasaki “thank you.” Wani kallo Anas ya watsa wa waiter’n take yaji wani bak’in kishi ya tokaresa ji yake kamar ya tashi ya shaqure sa ai shi yakamata ya yaba kyan da tayi ba wani daban ba, kuma yayi. “Can I have your number?” ya tambayeta, “zanso zama abokin ki.” “K’ato dakai?” Anas ya tambaya a fusace, “toh barata bayar ba. Ko kunya ma bakaji ma mschww! Boss naka zan kira yayi firing naka next time baraka sake cewa kanasan wata da abokanta ba, stupid kawai.” “Mr. Fauzi I’m so sorry dan Allah naga PA’rka ce am sorry please.” “She is not my PA she is my girlfriend.” “Omg! Mr. Fauzi please forgive me wallahi bansani ba.” “Damuwanka, Boss naka zan kira abincin ma mun fasa ci.” Wallet nasa yaciro ya irga kud’in ya wurga masa. “Fannah lets go” ya fad’i a fusace. Dakewa tayi, “Anas” ta kira sunansa cikin wani irin salon muryan da bata tab’a amfani dashi ba. “Calm down kaji? Calm down please.” A hankali yaji hankalinsa na kwantawa. “Calm down please” ta sake fad’i. Idanunsa da suka kad’a taga sun soma dawowa asalin farin kalansu. *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:50, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 3⃣7⃣ Ita bata ma san wace chef Khadeejan ba, tambaya ta rigayi har ta sameta sam ta kasa fad’a mata abinda ya kawo ta. “Kece Fannah Aleeyu PA’n Boss koh?” Khadeeja ta tambayeta ganin Fannah batada niyan magana. “Eh” ta fad’i fuskarta cike da tausayi da damuwa, baiwar Allah Khadeeja kuwa tun ganin Fannah tasan Boss ne ya turo ta tayi firing nata saboda glass cups da suka fashe mata d’azu. “Boss ne ya turoki kizo kiyi firing d’ina ko?” Ta tambaya nitse, kai Fannah ta d’ago ta kalleta cike da tausayi. “I’m so sorry Khadeeja inda inada yadda zanyi da nayi ki cigaba da aiki anan.” “Ba komai Fannah, ba laifin ki bane kema.” “Me kikayi ne?” “Glass cups guda biyu ne suka fashe min mistakenly d’azu.” “Kawai? Shine Boss zeyi firing naki?” Fannah ta tambayeta cike da mamaki. “Wallahi shine kawai kuma ma bada gangan bane dan Allah ki rok’a min shi wallahi na rasa aikin nan bansan ya zan ciyar da yara na ba, miji na ya gudu ya barni da kula da yaranmu guda biyu, please Fannah.” Fannah uwar tausayi har idanunta sun cike da hawaye. Ai wannan ba adalci bane ita cups nawa ta fasa masa, mesa bece zeyi firing nata ba se wannan baiwar Allar data fita buk’atar aikin. “Karki damu Khadeeja zanyi iya k’ok’arina inga kin rik’e aikin ki barin je in gwada masa magana, bar kuka kinji?” “A’a Fannah karki rasa aikin ki a sanadi na kibari kawai.” “A’a Khadeeja I insist in shaa Allah barin rasa nawa ba.” Ahaka ta fice daga kitchen d’in takoma last floor inda tayi knocking a bakin k’ofar office nasa da “enter” da yace mata ta bud’e ta shiga a daidai gaban table nasa ta tsaya. “Mr. Fauzi” ta kira sunansa kanta sunkuye. “Yes” ya amsa ta “kin gama duka aikin dana bakin ne?” “A’a” ta amsa tana kad’a kai. “Meh kike jira then? Ko so kike nazo in tayaki?” “A’a Mr. Fauzi batun chef Khadeeja ce-” katse ta yayi “aw! Bakiyi abinda nasakin ba kenan?” “Mr. Fauzi I don’t think its fair ayi firing nata.” Kallonta yake cike da mamaki, lallai ma! Jingina yayi jikin kujerar sa tare da crossing arms nasa. “Ke ya kamata ayi firing kenan ko?” Ya tambayeta tare da d’age gira. “Eh!” ta basa amsa tare da d’ago idanunta suna kallon juna. “Mr. Fauzi ni yakamata kayi firing ba Khadeeja ba, sau nawa nake fasa maka glass cups mesa bakayi firing d’ina ba se ita data fasa guda biyu kacal? Mesa barakayi firing d’ina ba?” katse ta yayi a fusace. “Dalili kison ji? Nima bansani ba Miss Aleeyu, kina musu dani, kina karya min cup almost everyday, kina fad’amin magana iya san ranki amman na rasa mesa nakasa firing naki.” Ya fad’i a fusace saboda shi kansa abin ya soma damunsa gashi daga ya zauna seya soma tunanin Fannah koda ransa a b’ace ya tuna da ita seya nemi b’acin ransa ya rasa. “Toh itama kar kayi firing nata please, be fair and just. Tunda baraka iya firing d’ina ba itama kayi hak’uri kar kayi firing nata please tunda duk d’aya muke aiki muke maka. Bada gangan ta fasa ba, in ka koreta daga nan batasan dame zata ciyar da yaranta ba, please consider this”,ta fad’i tare da sunkuyar da kanta. A hankali maganganunta suke shiga kunnen Anas. Tunda yazama CEO’n wannan Enterprise ba wanda ya tab’a ce masa ga abinda zeyi kokuma yayi abu ba haka akeyi ba se Fannah kuma yarasa meke damunsa ya kasa tsawata mata se kawai yaji yanasan yayi abinda ta buk’ace sa. “Je ki ce mata ta cigaba da aikin amman ta kiyaye nan gaba.” Fannah bata san sanda ta d’ago kai tana murmushi ba, bata d’au akoi tausayi cikin zuciyar Mr. Fauzi ba. “Thank you Sir, thank you so much” da sauri tafice taje ta sanar da Khadeeja, har hawayen jin dad’i sanda Khadeeja ta zubar, godiya sosai tayi wa Fannah, itama Fannan taji dad’i ganin ta farantawa ‘yar uwarta rai. Mr. Fauzi kuwa yana cikin wani yanayi wai mesa baya iya turning Fannah down? Mesa da ta nemi alfarma wajensa seyaji yanasan yi mata, mesa? Shi bayasan haka, yafisan yana k’untata mata yana sata kuka kullum baya san yana farinta mata kamar yadda yayi yanzu. “Damn it!” Ya fad’a a fili. “What is wrong with me?” **** Bayan Fannah ta isa mailroon ta cicciro mails na Mr. Fauzi tana tantance masu amfani da maras amfani, tana gamawa tayi disposing mara amfanin sannan ta nufa wajen Kacallah inda ta amso duk wani business transactions da meetings na Mr. Fauzi. Komi da komi ya dawo hannunta yanzu tunda itace PA’nsa. Kafin ta shiga office na Mr. Fauzi ta wuce nata dan rescheduling business trip nasa kamar yadda ya buk’ata in 2 months time. Daga nan ta wuce nasa office d’in tayi knocking yace, “come in” nan tashiga. Sede ta karanci yadda ransa yake a b’ace cikin d’an k’ank’anin lokacin nan. Toh meya samesa? “Sir nayi rescheduling trip d’in ga kuma mails nakan.” Ta fad’i tare da ajiye masa kan table nasa. Bece mata komi ba yaja mails d’in yana duddubawa bayan yagama dubawan ya d’ago blue eyes nasa “ina mail da Enterprise Bank suka turo min?” Hannu Fannah ta aza kan fuskarta tare da toshe bakinta. Wallahi kuwa taga mail d’in ta yasar dan be mata kalan me amfani ba. “Tambayarki nake ina yake?” “Sir I’m sorry na yasar.” Blue eyes nasa ya zaro, “kin meh? Kin yasar? Da hankalinki kuwa?” “Sir I’m sorry naga kamar-” bata k’are maganar ba ya katse ta cike da tsiwa “kinga kamar beyi kalan me amfani ba ko? Na baki nan da 5 minutes kije ki nemo min mail d’in duk inda kika kaisa. Mschww!” Tana b’ari tace, “Sir I’m sorry amman an riga anyi disposing.” “Meaning what?! Kije ki nemo min, I don’t care, get out!” Hawaye tajiyo yana ciko mata a ido a sanyaye ta juya ta sauk’o zuwa first floor tare da neman waje ta zauna tana kuka batasan a ina zata nemo masa ba bayan motan kwashe shara ya riga ya tafi. Tayi kusan awa d’aya a waje sannan tajiyo ringing d’in wayarta tana dubawa taga Mr. Fauzi d’agawa tayi ba tare da tace komi ba. “Kin samun ne?” ya tambayeta. “A’a” ta amsa a takaice cikin muryan kuka. “Kuma shine bara kizo ki fad’a min ba? Come right away.” Nan ya katse fuskarta taje ta wanke sannan ta shiga elevator zuwa office nasa. Kallonta yake sannan ya karanci kuka taje tayi, sekuma yaji wani iri besan mesa ba presence na Fannah affects him yanzu. “Make me coffee and leave, na sallameki na yau.” Dad’i sosai taji amman bata nuna masa ba, nan da nan ta had’a masa cikin flask sannan ta fice. Bayan ta fita ya taso ya zuba kad’an cikin cup tare da zama kan kujera, seya kai coffeen baki seyaji kuma bayasan sha, wayasani ko san dayake ma coffeen ta ne yasoma dawowa kan Fannah. “No way!” ya fad’a a fili. Coffeen ya mayar cikin flask d’in shi a dole ya fasa sha bada jimawa ba yatashi yasake juyewa cikin cup duk yadda yayi ya hana kansa ya kasa he is already addicted to it. Shima bada jimawa ba ya rufo office nasa yayi tafiyarsa, instead yaje gida seya wuce paint house nasa ba tunanin abinda yakeyi sena Fannah ya rasa meke damunsa kwalban giyansa ya d’auko ze sha abin mamaki ya tsaya cak kalamun Fannah na yadena shan giya yasoma yawo masa a k’wak’walwa. “Damn it!” Ya fad’i tare da rufewa ya mayar cikin fridge d’in. Toilet ya nufa ya rage kayan jikinsa tare da kunna shower ruwa na sauk’a jikinsa. ***** Fannah kuwa tun isarta gida ciwon mara ya rik’e ta alaman wata ya zagayo kenan, haka tata fama da ciwon gashi kuma tak’i shan magani. A haka har bacci ya saceta a wahalince. Cikin baccin ta soma yin mafarkinta na kullum akan wanda yayi raping nata yadawo ze sake mata. Firgit ta farka ta soma kuka tana ihu Mami dake tsakar gida ne tashigo a guje da k’yar tasamu tayi calming Fannah tayi hugging nata. “Ya isa Habibti ki cire wannan abu daga ranki, ace yau shekaru nawa sede baki kwanta ba zakiyi mafarkin abin. Ya isa haka mana.” “Mami wallahi inaji mutumin ya matso kusa dani wai yana *_TARE DA NI_* Mami tsoro nakeji.” “Shhh! ya isa mafarki ne in shaa Allah kin rabu da mutumin har abada bashi ba ke, kinji? Ya ciwon marar?” “Mami har yanzu yana min ciwo.” “Toh kink’i shan magani ba dole ba, kin kwan biyu bakiyi ciwon ba ma ai Allah kawo sauk’i deh, sannu ki huta in jikin be sake kiba gobe barakije aiki ba.” Sanyi sosai Fannah taji har cikin ranta, gobe barata je aiki ba. Washegari Anas ya tashi da coffeen Fannah yayi breakfast sannan ya nufa office shiru shiru har 8:30AM Fannah bata zo office na “lallai ma yarinyan nan ta gama raina min wayo” yace a ransa tare da ciro wayarsa ya kira lambarta. **** Afrah ne zaune kan Fannah suna hira, sosai Fannah taji sauk’i saboda Mami ta tilasta mata sanda tasha maganin jiya amma da taga Mami seta shangwab’e wai jikin ba sauk’i. Wayarta ne ya soma ruri aiko tana kai kallonta kai taga Mr. Fauzi “ungo Afrah gashi ki d’aga kice masa banida lafiya ne kinji? Zan baki 1k kisa kati.” “Dagaske?!” ta tambaya tana washe hak’wara. “Na rantse” Fannah ta tabbatar mata, ai karap ta d’aga wayar Anas yayi niyan fara suburbud’o mata masifa kawai seyaji muryar da ba nata ba “hello Mr. Fauzi.” “Hello” yace cikin sanyin murya kamar ba shi ba. “Afrah ce?” Sanda tasa a handsfree sannan tace, “eh ina kwana Mr. Fauzi?” “Lafiya call me Ya Anas kinji?” “Toh Ya Anas, kaji Ya Fannah shiru yau ko? Batada lafiya ne.” “Batada lafiya meya sameta?” gabad’aya yaji ya damu, a tunaninsa ko hannunta ne da yata sata rubutu jiya yayi worse.” “Menstral cramp (mp) ne” ta amsa sa a takaice. Bugi Fannah takai mata a cinya “bakida hankali ne?” Ta fad’a k’asa k’asa yadda Anas bareji ba. “Toh meh ba MP’n bane?” Afrah ta bata amsa itama chan k’asa k’asa. “Uhmmm toh kun kaita asibiti?” Ya tambayeta shi kansa yaji kunyan zancen. Itama se yanzu taji kunyan abinda ta fad’a masan. “A’a” ta amsa cike da kunya. “Toh yanzu zan turo mota se a kaita kinji? Ki sanar da Mami.” Kai Fannah take kad’a mata da nufin tace a’a. “A’a Ya Anas karka damu tasha magani yanzu haka ma tana bacci.” “Are you sure Afrah?” “Eh Ya Anas gobe ma in shaa Allah zata dawo office.” “Toh yayi kyau bye.” Yayi hanging. “Bakiyi ba wallahi Afrah taya zaki che masa MP ke damuna? Da wani idan kikeson in kallesa gobe mschww! ni wallahi barin koma office ba.” “Toh meh? Kefa kikace yanada k’anwa ai itama nasan tanayi, kuma mahaifiyar sa ma tanayi me abin jin kunya? Amman fa Mr. Fauzi I mean Ya Anas ya damu da lafiyarki, ko ince yana sanki ma, baki ji yadda ya damu bane?” Shiru Fannah tayi bata tanka ta ba tunanin ya next meeting nasu da Anas ze kasance kawai take wannan kayan kunyan da Afrah ta mata. Ta fannin Anas kuwa ya kasa gane kan ranan gabad’ai coffeen data had’a masa jiyan ma ya shanye tas, haka kawai yaji yana san sata a idanunsa, yau da be ganta ba seji yake kamar yayi asaran wani abu a jikinsa. Hannayensa biyu yasa cikin gashin kansa yana hargitsawa. “What is wrong with me? I am not missing Fannah, I’m just missing her coffee, thats all.” Model nasa ya ciro dan cigaba da yi ko ze d’an manta Fannah da coffeen t, yana aza hannu kan model nasan se tunanin Fannah ya b’ullo masa akai. “Damn it!” Yayi wurgi da super glue dake hannunsa. A fusace ya mik’e ya nufa wajen fridge nasa yaciro kwalba d’aya daidai ya bud’e yakai baki se kawai kalamun Fannah suka soma masa yawo akai. “Ohh!!! What is wrong with me?” Ido ya rufe yasa kwalban a bakinsa sanda yasha rabi sannan ya ciro. D’akinsa ya nufa ya mik’e kan gado nan ma be bar tunanin nata ba musamman ma dayaji bata da lafiya yasha ganin yadda Amal ke kuka in menstral cramp yakamata. Haka yayi yayi amman ya kasa bacci, meeting dayake dashi kawai ya tashi ya shirya. Driving ma kasa yi, tuk’asa driver yayi. Ko a wajen meeting d’in yakasa concentrating, har aka tashi besan me suka tattauna akai ba, mutanen kuwa sun karanchi hakan, koda suka tambayesa menene che musu yayi kansa ke ciwo. Daga chan ma gida yasa driver ya wuce dashi sosai Ummie, Amal da Shettima sukaji dad’in dawowansa, Abuu bai gida da yayi murna shima dan d’an kwana biyu da Anas yayi ba’a gida ba ya fitinesa. Da k’yar Ummie ta ja Amal waje daga d’akin Anas dan barin sa ya huta, bada dad’ewa ba Shettima ya shigo har ya zauna Anas beyi noticing ba, sanda ya tab’a sa sannan firgit ya juya yana kallonsa. “Maza yaushe ka shigo?” Ya tambayesa cike da mamaki. “About a minute ago tunanin me kake? Tunanin abinda Abuu ya fad’a maka shekaran jiya ne?” Shi Anas ya ma manta da wan can batu, se yanzu da Shettima ya tunatar masa. “Shettima ni bansan ina zan samu mace in kawo wa Abuu ba I don’t trust in love.” “Ya Anas dade kayi hak’uri ka duba cikin ‘yan matanka wacce tafi hankali ko a aura maka Falmata.” “Hankali? Ai dukansu bame hankali, they are after my look and money, ba wacce take sona tsakani da Allah saboda kud’i na da kyau suke bina. Ni nasani ba macen da zata tab’a sona tsakani da Allah.” “Akoi Ya Anas kuma ina kan maka addu’a, Allah bayyano maka da ita nan da wata shidan da Abuu ya yanka maka. Macen da zata soka tsakani da Allah, wacce bara ta damu da kud’inka ba, ko kyanka ba, wacce barata damu da duniya da abinda ke cikinta ba, she’ll be a decent girl wanda bata shirin batsa ba kuma ruwanta da jan attention na mutane, me tarbiyya da hankali da kuma ilimi, wacce zata na maka wa’azi duk sanda kayi ba dede ba” Duk wannan halaye da d’abi’un da Shettima ya lisafo se Anas yaga sak na Fannah kenan. Yaci ace a iya zaman sunnan ta fito tace tana sansa kamar yadda receptionist na sa ta masa da sauran ma’aikatan sa, koda ya bata iphone cewa tayi bataso dan bata da option ne yasa kawai ta amince ta karb’a meaning bata damu da kayan duniya ba kenan. “NO!!! SHE CAN’T BE THE GIRL” ya fad’i a fili ba tare dayasan yayi hakan ba. “Wace yarinya kenan Ya Anas?” Shettima ya tambayesa. “Yarinya kuma?” Anas ya wayince. “Wace yarinya? Waye ya kira wata yarinya anan?” “Kaifa kace ‘no she can’t be the girl’ yanzu. Wata yarinya kak nufi kenan?” “Kai kacika suratan banza wallahi ni tashi kabani gu, inji da problem dake damuna na neman matan aure in 6 months time.” Se da Shettima yakai bakin k’ofa sannan yace, “Ya Anas kode Fannah ce?” “What?!” Pillow ya d’aga ya wulla masa wanda tuni ya fice yana masa dariya. Mesa hankalin Shettima ze karkato zuwa kan Fannah? Mesa se ita? To kode na fara santa ne? “No way” ya fad’i a fili. “I can’t love Fannah, mezanyi da ita? Coffeenta kawai nakeso ba ita ba, kuma shi d’inma daga yau nadena sha. I can’t fall for Fannah.” *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:50, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 4⃣8⃣ _5:00AM_ Shettima ne ke knocking bakin k’ofan d’akin Anas, bacci Anas yake sosai wanda ya jima beyi erinsa ba ko jin knocking d’in baiyi. “Bam bam bam! Ya Anas katashi Asubah yayi.” Cikin gigin bacci yace, “naji seka b’alla k’ofan neh?” “Ya Anas bazaka masallaci bane?” Shi se yanzu ma ya tuna ana zuwa masallaci bayan na juma’ah. “Barinje ba zanyi a gida.” Dama amsan da Shettima ke jira kenan, Ya Anas baisan zuwa masjid inbanda na juma’ah daya zamo masa dole sekuma in Abuu ya tilasta masa. A sanyaye ya juya Abuu dake tsaye a parlour yana jiransu ya tambaya, “ya ina wan naka?” Qarya Shettima ya masa, “wai kansa ke ciwo zeyi a gidah.” “Toh Allah sawaqa.” Da “Ameen” da Shettima ya amsa sa suka fice. Se 5:15AM Anas ya tashi yayi sallah bacci ya koma se 7:00AM ya tashi ya soma shirin office yau kawai yaji yanasan sa jampah kasancewar yau Juma’ah. B’angaren da yake adana jampopin nasa ya bud’o suna nan turum ba adadi, dubawa yake chan yaciro wani sky blue half jampa yasa, se inche tunda nasan Mr. Fauzi be tab’a yin kyau kamar na yau ba, ba k’aramin amsar kayan yayi ba, cufflinks nasa masu tsada yasa. Fefes yafita bayan yagama feshe kusan rabin designer turarukan sa, jakar laptop nasa ya saqalo daidai yafito yaga Abuu zaune kan dining yana shan coffee. Cike da girmamawa yagaishe da Abuu tare da nufan dining space d’in shima dan had’a tea. “Ya jikin naka?” Ya tambayesa. Jiki kuma? ya tambayi kansa kode qaryan da Shetitima yayi dan rufa masa airi batun zuwa masjid d’azu kenan? “Da sauk’i.” ya amsa. Good, Anas I hope kana tsokaci da lokacinka, yau sati d’aya ya tafi cikin 6 months dana baka, kasani ko minti d’aya barin k’ara maka akai ba.” Ko uffan Anas bece masa ba, amman take blue eyes nasa suka k’ada ransa ya b’aci, se faman had’a tea’n sa yake. “Anas dakai nake magana.” “Naji” yace tare da ajiye flask d’in, tean ma ya fasa had’awa ya gommaci ya tafi da yunwa. Ficewa kawai yayi ransa na tafasa. Yawonsa ya fice se to 8 ya isa office ko amsa gaisuwan da ake masan ma beyi. Ganinsa cikin jamfa duk ya basu mamaki se kallon sa suke. “Sir you are looking awesome” cewar Mubarak. Wani kallo Anas ya watsa masa. “You are fired!” Ya daka masa tsawa. “Sir I’m sorry dan Allah kar kayi firing d’ina.” Bello dake gefensa ya basa tausayi. “Sir he is sorry please, consider this.” “Kaima kanada bakin magana kenan? Follow him you both are fired kuje ku samu Adam.” Nan ya nufa wajen elevator’n sa ko ya akayi yaga d’an wani stain kan floor d’in oho. “Wa yayi mopping floor d’innan yau?” Baki na b’ari Abdul Hamid dake gefensa yace, “Boss Yakurah ce.” “Jeka sameta and tell her she is fired inform Adam yayi replacing nata now, am I clear?” Baki na b’ari yace, “yy..yyes sir” nan Anas ya haura zuwa office nasa se huci yake shikad’ansa gawani uban yunwan dayakeji dan rabuwansa da abinci tun jiya da rana. ***** “Ya Fannah kisa wannan d’in mana wallahi yayi kyau kuma ai Ya Anas zeji dad’i idan ya ganki dashi tunda shi ya siya miki.” Cewar Afrah tana mik’a mata wata electric blue gyale. “Banaso! Ha’an! Barin sa,ba kema kinsan ba burgeni gyalen nan yake ba, hijabi na mutunci na.” “Haba mana Ya Fannah ace saurayinki ya siya miki abu kik’i sawa? Gaskia ba haka ake soyayya ba.” Kuma fa haka ne, Fannah ta fad’i a ranta, inhar ta cigaba da behaving bata damu da Mr. Fauzi ba definately Afrah da gane ganenta zata gano bakin zaren wataran. Kai amman kuma bata so, bata son sa gyalen. “Barin sa ba ki miyar” ta bata amsa tana k’ok’arin ciro hijabinta daga cikin drawernsu, daidai lokacin Mami tashigo. “Ya Fannah amshi kisa mana.” Cewar Afrah. “Meke faruwa ne?” Mami ta tambaya tana k’arisowa cikin d’akin. Kafin Afrah tayi magana Fannah ta tareta “ermm babu komai Mami dama Afrah na tambaya ko gyalen hannuntan ya tafi da kaya na.” “Eh sosai ma ya tafi, yau kuma gyale za’a sa neh?” A kunyace tace, “eh mana Mami ko kin manta Anas ne ya kawo min.” “Toh yayi kyau Allah kiyaye hanya.” “Ameen Mami.” Gyalen ta amsa gun Afrah dake mata murmushin tsiya yafawa tayi harda rufe kai dashi. “Haba Baaba, meh haka sekace goggo? Ai tsofi aka sani da yafa gyale haka kawo kiga.” Nan Afrah ta tsara mata gyalen sosai tayi kyau. “Meh haka?” cewar Fannah tana kallon kanta jikin madubi. “Sekace neman miji zani? Batsan yayi yawa mana Afrah.” “Wallahi beyi ba Ya Fannah, dan Allah karki b’ata kibari a hakan.” Da k’yar Fannah ta yarda ta fice, tafi minti biyu tsaye bakin k’ofar Enterprise d’in amman takasa shiga se kunya takeji. Da k’yar ta iya ta shiga Yusuf ta soma tararwa da sauri ya nufi kanta “Fannah barka da kika zo! Dan Allah kije ki ba Boss hak’uri wallahi da safen nan yayi firing mutane uku.” “Mutane uku?” Fannah ta zaro ido. “Dalili?” Nan ya labarta mata komai... “kinsan haka yake in ransa a b’ace, please talk to him.” “Karka damu I’ll try.” Nan ta haura sama, jan bakin da Afrah tasa ta sawan dolen ta sa hannu tana gogewa sede koda ta ciro madubi ta duba taga yana nan kan yanzu ta shafa saboda 24hours ne. Tsuka taja, a hankali tayi knocking bakin k’ofar san. “Enter” yace. A hankali ta waina k’ofar ta shiga alokacin ko juyawa yaga waye ne beyi ba as ya zage se masifa yake kan wayan da yakeyi. Kallonsa Fannah ta tsaya yi dan yadda jampan jikinsan ya mugun amsar sa bata tab’a ganinsa da jamfa ba kuma setaga kamar jampan ma yafi amsar body figure’nsa. A’a to kodan bata tab’a ganinsa dashi bane? Wow! amman gaskia yayi kyau kasa kallonsa tayi musamman yadda gashin kansa ke sheqi. “Fire them dukansu ukun, fire them and replace them with better ones, am I clear?” Ding! Ya katse wayar. Nan ne ya juyo dan ganin ko waya shigo. A hankali blue eyes nasa suka sauk’a kan Fannah kallonta ya tsaya yi dan wani kyan da tayi, daga kan d’aurinta, yadda ta yafa gyalen, lace d’in jikintan, d’inkin da komai ya masa kyau. Fuskarta kuwa ba inda yakaisa yin kyau, dark red jambakin da tasa ba k’aramin haska skin nata yayi ba. Kallonta yake itama tana kallonsa duk suna admiring kyan junansu sekuma gashi kamar sun had’a baki duk suka sa blue kaya sede nashi light nata dark. Haushin da Abuu ya tusa masa ya nema ya rasa daga ganin Fannah. Ita ta fara kau da kai sannan shima ya kawar. A hakali ta tako izuwa gaban table nasa “good morning Mr. Fauzi.” Ta gaishesa beko amsa ba, kallonta kawai yake kai ta d’ago a hankali tana kallonsa taga shima ita yake kallo kuma koda suka had’a ido beji kunya ya kawar da idanunsa daga gareta ba. Ganin kallon bana k’arewa bane tace, “ermmm let me make you coffee sir./ Be ce mata komai ba ta juya. 2 minutes later ta gama had’awa ta kawo masa tare da ajiye wa agabansa. Ganin baida niyan sha tace, “please take it sir” magana take masa a hankali dan abinda Yusuf yace mata kan ran Boss a b’ace yake yau. Sip d’aya ya kai baki tana tsaye a kansa. “Sir” takira sunansa cikin siririyar muryarta. Be amsa ba illa dawo da kallonsa dayayi a gareta. “Ermmm nace can you do me a favour?” Shiru yayi chan yace, “what is it?” “Sir please kadawo da wad’anda kayi firing... Please.” “No barin dawo dasu ba, bana son shisshigi, just make me coffee and leave ga chan flask d’in achan” ya nuna mata da yatsa. “Please fa nace, do this for me please, will you?” “No Miss Aleeyu, they are useless workers sesa nayi firing nasu.” “Sir saboda ance maka kayi kyau? Is it a crime? Yanzu nima in nace maka kayi kyau sekayi firing d’ina?” Ta tambayesa, shiru yayi bece komai ba. “Toh Mr. Fauzi kayi kyau yau, kayi kyau sosai. Is that it? Fire me toh.” “No Miss Aleeyu stop it! I can’t fire you, I just can’t.” “Why Mr. Fauzi? kamar yadda suke mutane nima haka nake, abinda zaka musu shi zaka min, be fair please.” “No Miss Aleeyu, you are diffrerent, kidena had’a kanki dasu. Kina min abubuwa da dama dayaci ache nayi firing naki amman I can’t.” “Toh kayi hak’uri ka dawo dasu please kaji Mr. Fauzi? Yi hak’uri this job is their only source of income yi hak’uri zasu kiyaye nan gaba.” Shiru yayi bece komai ba kuma bayida niyyan magana. “Mr. Fauzi must I beg on my knees zaka dawo musu da aikinsu? I’ll do it.” “No don’t! Zan dawo musu da aikinsu, don’t kneel.” Yayi warning nata dad’i taji sosai. “Sir are you serious?” “Yes kije kice Adam ya dawo dasu.” Cike da jin dad’i tace, “thank you sir, thank you” nan ta fice taje ta sanar da Adam godiya duka suka riga mata kamar su cinye ta. Bada jimawa ba ta dawo office na Anas. Coffee ta had’a masa cikin flask sede duk sanda ta d’aga kai ta kallesa shima ita yake kallo, har ya soma sata feeling uncomfortable. Gyalen nata tayi yunk’urun d’agawa zuwa kanta. “Stop, kibarshi haka” yace da ita. Yi tayi kamar bata jisa ba, se k’ok’arin d’agawa take. “Miss Aleeyu as your Boss and boyfriend I said stop it, okay?” Ya fad’a a tsawace nan ta bari wayarta dake side bag nata ne ya soma ringing nan ta ciro ganin Yusuf ke kira ta d’aga a takaice. “Hello?” On the other side yace; “Our life saviour!” Murmushi ta saki wanda yasake fidda kyanta. “Kai dan Allah, ba komai don’t worry.” “Dama kira nayi dan na sake miki godiya and to offer you a lunch saboda in sake nuna miki godiyata.” “Haba Yusuf is it necessary?” Duk wannan waya da takeyi Mr. Fauzi na zaune yana kallonta wani kishi yaji wanda be tab’a feeling ba ya tokaresa jin ta ambato sunan Yusuf wato dashi ma take wannan murmushi sekace an mata albishir d’in shiga aljannah, lallai Yusuf you wanna die ya fad’i a ransa. “Awwn! Lunch zaka siya min?... Aww tare zamuje muci?... Are you sure?... Toh nagode zan sauk’o yanzu... Thank you.” Nan ta katse wayar. “Mr. Fauzi zan tafi dama had’a maka coffee kace inzo yi nayi zan tafi, se anjima.” Bece mata komai ba as tunanin wani aiki ze bata tayi dan hanata fita da yake. Chan ya duba gaban table nasa yaga wasu mails da Kacallah ya kawo masa jiya wanda za’ayi reprinting nasu. Har takai bakin k’ofa ya kira sunanta “Miss Aleeyu!” Chak ta tsaya tare da juyowa. “Yes Sir?” “Come” yace da ita ba musu ta k’ariso. Pen da plane sheets guda goma ya irga ya mik’a mata tare da had’a mata da mails guda goman. “Gashi min copying wad’annan da neat handwriting don’t make any mistakes.” Kallon papers d’in ta tsaya yi sannan takoma kan Anas. “Mr. Fauzi kai kace fa am nomore your PA kuma yanzu kana bani aiki?” “Yes Miss Aleeyu, na canza mind d’ina ne yanzu in aiki ya taso zan iya saki tunda mu bibbiyu ne kawai, kiyi sauri I need them ASAP.” “Ayyah Mr. Fauzi kaifa kace ba aiki yanzu kuma...” Katse ta yayi “hurry Miss Aleeyu yau Juma’ah ne zanje masjid.” “Toh Mr. Fauzi ayi printing nasu mana ba sena rubuce su ba.” “Yes Miss Aleeyu rubuce su nakeson kiyi hurry up go and sit acan.” Zata sake magana yace, “now!” A d’an tsawace. Batada wani option haka taje ta zauna tafara copying tana rubutawa. Kallonta yake. Daidan ki kenan se muga ya ke da Yusuf d’in zaku fita lunch. Yace a zuci. Huh! Nima yunwa nakeji bari ta gama muje muci breakfast/lunch tare daga chan sena wuce masjid. *kuyi hak’uri abinda yasamu kenan yau* *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:50, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 3⃣8⃣ Washegari tun Asuba Anas ya tashi saboda kasa bacci da yayi ga kuma rashin abin shaye shayen sa kusa dashi, koda na kusa dashin ma se yayi drama yake iya sha yanzu tun maganan da Fannah ta masa har yau yakasa erasing daga memory’nsa. Bayan yayi wanka ya shirya yafito already Ummie da Amal sun had’a masa breakfast, as usual shida Amal suka karya sede yau Anas ya zage yaci abincin sosai sab’anin yadda ya sabayi danko in be sha coffeen Fannah ba bai iya breakfast me kyau. Se forcing kanshi yake yana ci shi a dole yanasan mancewa da coffeen, a tunanin sa in ya dena shan coffeen ta ze iya mancewa dashi, eventually Fannan ma ze manta da ita seta zama missed call. (LOL) “Wai! wai! wai! Ya Anas ai ka cinye abincin bani yau.” Murmushi ya mata tare da rufa bakinsa ta hanyan aza hannunsa kai. “I’m sorry Angel yunwa nakeji. Nikam kunyi waya da Fannan office d’ina jiya?” Shiru tayi bata amsa saba gudun karya masifeta. “Angel I’m talking to you.” “Ya Anas kayi hak’uri.” “For? Amsa min tambayan dana miki mana kunyi waya jiya?” Kai ta giad’a a hankali cike da tsoro saboda Anas ya hanata waya da Fannah. “Meh tace miki?” Nan ma shiru tayi. “Feel free and tell me barin miki komai ba kinji?” Ya d’ago hannunta yasa cikin nasa. “Promise Ya Anas baraka sake hana ni waya da ita ba?” “Yes Angel I promise.” “Tacemun batada lafiya mentral cramp yana damunta.” “Tace zata office yau?” “Tace min baza ta ba wai seta warke gabad’aya.” Kai ya giad’a tare da kewayo da kallonsa daga kan Amal zuwa kan plate na abincinsun “in ta haka menstral cramp d’in da wahala kenan.” Ya fad’i wa kansa kasancewar Amal na kusa dashi seta jiyo sa. “Sosai Ya Anas ni in ya tashi min ji nake kaman zan mutu.” Murmushi ya mata “bara ki mutu ba ma in shaa Allah barin wuce office kinji?” Kai ta giad’a masa a yayinda ya bata peck a goshi. “Ummie thank you for the breakfast na tafi” yache da d’an ihu dan Ummin dake kitchen ta jiyosa. “Adawo lafiya Babana” ta mayar masa itama da ihun. As usual k’arfe 8:00AM yayi masa a office nasa, Kacallah ya kira ya tambayesa ko yanada meeting yau. Unfortunately Kacallah yace masa ai duk wani schedule nasa na wajen Fannah. “Toh mesa ka bata duka?” “I’m sorry Boss but she is your PA, aikinta ne yanzu.” “Toh naji” yayu hanging. ***** “Mami ni wallahi barinje office d’inba, barin sake komawa bama gabad’aya. Bakiji me Afrah tace masa jiya bane? Che masa tayi wai MP ke damuna.” Baki Mami ta bud’e tana kallon ikon Allah. “Lallai fa Fannah se akayi ya? Abune kowace mace tanayi, basuda mata ne a gidansu? Shi kansa ya riga yasan mene, ni banga abin jin kunya ba a nan ba.” Can k’asa k’asa Fannah tace, “ai dama baraki gani ba.” “Nima de wallahi Mami” cewar Afrah. “Kekuma Afrah kika kuma wannan rashin hankali zan sab’a miki, Aiman ce yakamata tayi wannan sokanci ba ke ba.” Mami tayi lecturing nata. Juyawa Fannah tayi tana mata gwalo a dole an mata masifa itama. “Ke kuma Fannah sa hijabinki ki fice kinga already kin makara kuma Anas baya san latti.” “Kar yason” tace a k’asa k’asa. “Maza- maza! Tashi ki fice Fannah kar muyi fad’a dake da safiyan nan ko inje in sanar da Babanku ne?” “Allah sarki Mami dan Allah mana, gobe zanje I promise.” “Wannan kuma ke ya dama Afrah taho muje ki tayani shirya kayakin Aiman.” Da gwalon da Afrah ta ma Fannah tasa kai tabi Mami suka fice. Se zumbure zumbure Fannah take ita jiya da bata sa Mr. Fauzi a ido ba, ta wuni lafiya ba tashin hankali amman tasan definately suka had’u yau seya sata kuka, ita da ana shan maganin hana zuban hawaye da tasha. Ganin ba mahallici se Allah yasa kawai taja blue hijabinta me torches fari tasa, ta d’au jakarta ta sak’ala tare da cikasa da duk wani abinda zata buk’ata sannan ta fice ko sallama batayi dasu Ba ita ta isa office ba 8:34AM. Tana tsaye gaban office na Mr. Fauzi amman ta kasa shiga seta d’aga hannu zatayi knocking setaji kunya, yanzu yau wani irin kallo ze na mata? “Mschww Afrah ba kiyi ba wallahi” ta sake nanatawa for the hundredth time a zuciyarta. Ai haka ta kasa shiga office nasan, daga k’arshe nata ta zarce kawai taje ta had’a masa schedule (kamar time table haka) na ranan, tayi arranging komi, meeting d’aya yake dashi se mutanen da zasu zo ganinsa na signing contract guda biyu, sekuma na siyan shares na Global investments. Tagama ta ajiye a gefe guda chan ta ciro wayarta tana game itade yau barata had’a ido da Mr. Fauzi ba sekace wanda tayi sata. ***** Anas kuwa yakasa tsinana wa kansa komai banda tunanin Fannah wai anya yau inbe sata a ido ba ze iya kwanciya lafiya kuwa? “Oh No! No! No! Why am I acting in this way? Coffee nake missing ba Fannah ba, coffee ne” ya tunar wa kansa. Ai daga k’arshe kasa hak’ura yayi ya tashi ya nufi office na Fannah koda bare ganta ba yau yaga office nata he is okay with it. Fannah na cikin game taji an murd’a hannun k’ofar office nata ido tasa wa k’ofan jiran ganin ko waye dukda kuwa zuciyar ta na sak’a mata wai Yusuf ne. Wayar ta tayi wulli dashi da suka had’a ido hud’u da Anas dama dalilin dayasa ta sako hijabi me hula kenan yau, da sauri sauri taja ta rufe fuskarta. Yin hakan seta tuna masa da incident na jiya seya gano dalilin dayasa take rufe fuskar kunyan sa takeji dan Afrah tace masa MP ke damunta, shi kansa kunyan ta yakeji bama batun MP’nta ba. In kuma tace meya kawo sa office nata fah? Karkuma tagane dan yana missing nata ne yashigo ta raina sa. Ganin batada niyyan magana yasa yayi giaran muryar. “So kinzo shine baki sanar dani ba? Nazo picking wani file ne dama” yayi k’arya yana wani basarwa. Da k’yar ta iya bud’e baki ta gaishe sa. “Good morning, wani file ne?” ta tambaye sa cikin siririyar muryarta. Rashin sanin wani k’aryan ze sake mata kawai yace, “to my office” chike da isa. Yana fita ta d’ago kai “to my office” ta kwaikwaye sa sannan tad’au jakarta da jotter’nta da pen da pencil tabi bayansa. Bayan like minti d’aya da shigan Anas office nasa Fannah tashigo itama kanta sunkuye a k’asa daidai gaban table nasa ta tsaya tare da mik’a masa jotter’n gabansa “here is your schedule for today, inda akoi abinda za’a giara let me know” D’agawa yayi ya dudduba yaga komai yayi, yaga ta ma fi Kacallah iya amfani da lokaci dan kuwa by 2:30PM ya gama komai nasa yau. So yake ya tambayeta ya jiki amman kuma girman kai irin nasa bare barsa ba seya bud’a baki zeyi magana se wani abu ya katse sa. Itako tana nan tsaye kansa har yanzu tana jiran amsar sa in da akoi abinda be masa ba yafad’i seta giara. Can k’asa k’asa almost kamar da kansa ma yake magana yace, “ya jikin ki?” Fannah kuwa taji sa amman dan yadda mamaki yaso kasheta se kawai tace hala kunnenta ke mata k’arya yaushe Mr. Fauzi ze tambayeta ya jiki? Karkuma tayi shiru yace ta rai na sa yasoma balbaleta yanzu a nan, dan haka tace, “eh? Excuse me” fuskar nan a rufe da hijabi har yanzu. “Ya jikin ki nace” yasake nanatawa with thesame voice level dayayi d’azu. Se yanxu ta tabbata ba yaudarar ta kunnenta suke ba. “Da sauk’i” ta amsa a hankali duk seji take kamar ta nitse k’asa dan kunya. Da k’yar tayi managing tace, “thank you.” “Bana buk’atar godiyar ki” ya fad’i mata gatsau sekace bashi yanzu yayi magana a hankali ba. Itafa har yau ta kasa gane hali irin na Mr. Fauzi yanzu yanzu seya mata mutunci take wajen kuma ya zagesa yadda yaga dama. Juyawa tayi ta nufa wajen coffee machine dan had’a masa ai bata soma ciro cup d’in ba ya jefa mata tambaya. “Me kuma zakiyi acan?” “Had’a maka coffee sir.” “Banaso, bana buk’ata just kitafi kije office naki if am in need of anything I will let you know.” Wai yau Mr. Fauzi ne ke fad’in baya buk’atan coffee to kode wanda ta had’a masa jiya beyi dad’i bane kasancewar zogin da hannunta yake mata. Shi kansa be zata ze iya fad’in baya buk’atar coffeen ta ba se gashi ya fad’a confidently ma kuwa. “Sir indan na jiya beyi dad’i bane I apologise hannu na ke ciwo, will make it better yanzu.” “Banaso nace just get out kuma na hanaki ja min wannan hijabin kina rufe fuskarki dashi, me kike dashi da banida? Ja hijabin baya.” Dakewa tayi tak’i ja seda ya daka mata tsawa “ja nace!” Tana b’ari ta giara “now leave” a sanyaye ta juya ta fice tana isa office nata ta zauna kan cushion. “Mschww wallahi Mr. Fauzin nan kanada mental illness, yanzu kama mutum mutunci da ‘yan mintuna kuma ka koresa kaman kashi thank god kai kazo har nan ka kirani bani na kai kaina office nakan ba. Wallahi kawai dan na danne zuciyata ne da nayi kuka, sede kata wa mutane masifa kai aikin ka kenan, Allah shirya wallahi ina tausaya wa matar da zata aure ka” (ni miemie nace kina tausaya wa kanki kenan) “ace kullum masifa, masifa. Ni barin cigaba da yin game d’ina ma.” Wayarta ta ciro tacigaba da buga candy crush. Kusan to 12:30PM Anas ya danna mata kira ta telephone kan ta shirya zasu meeting. Yau akeyinta ita gaskia bata shirya zuwa meeting ba amman ya ta iya? Bayi ta nufa tayi changing sannan tafito tak’i shiga office nasan ma bale ya mata korin kare kona akuyan daya saba mata. Bayan like 5 minutes Anas ya fito taga ya canza shirinsa yasa navy blue suit, white shirt da ocean blue tie sosai kam yayi kyau ga yadda gashinsa yasha giara kafin ya kamata tana kallonsa tayi saurin kau da kai, bece mata komi ba koda yaganta tsaye bakin office nasan juyawa yayi ya soma tafiya a yayinda take binsa a baya. Driver ne ya tuk’asu har hall da za’ayi meeting d’in sun iso da shiga ya juya ya kalleta “sauran yau ma kiyi tsaki kokuma ki baje kina bacci kinji ba Miss Aleeyu?” “Naji” tace ba tare da ta kallesa ba. Kamar ranan yana shiga mutanen suka tashi masa bayan sun gama gaggaisa wa ya zauna a kujerar tsakiyan nufin shine babba ma a meeting na yau kenan. Duk abinda ke gudana Fannah ta kasa kunne tana sauraro tare da jotting down major points kuma, gajiya tayi da tsayuwan ta zauna still hankalinta na kan meeting d’in. Time to time Anas yake d’ago kai yana kallonta sam idanunsu basu had’u ba. Se 2:30PM suka k’are boring meeting d’in, indagin Fannah yayi tsami dan zama bayan sun shiga mota ya tambayeta, “ina abubuwan da kikayi jotting?” Cikin jakarta tasa hannu ta ciro jotter’ta tare da mik’a masa. Se kuwa yaga duk important abubuwan da sukayi discussing akai na had’a kan Flames Enterprises da C&C Enterprises duk tayi jotting down da kuma abubuwan da zasu amfanar da juna dashi, sosai kuma yaji dad’i. Amman meya kamata yayi wa Fannah? Godiya koba haka ba? But saboda dan girman kai irin nasa ya kasa, “nan gaba in ana meeting seki dena frwoning fuskarki ai kowa yasan meeting d’in ba dad’i gashi ki ajiye zan buk’ata anjima.” abin da yace da ita kenan. Sanyi taji sosai a ranta da beyi complaining akai ba amman kuma yak’i mata godiya dan uban girman kai. Sede abin da ta lura yau shine besa an k’ure AC kamar na ranan ba, kad’an kawai yasa driver ya kunna. Shikuwa Anas yayi hakan ne saboda batada lafiya, bayasan ya k’ara mata wani rashin lafiyar akan wanda take fama dashi, tunda ya karanci bame san sanyi che itaba. Yauma daidai gaban wata makekiyar hotel driver ya tsaya tare da bud’e masu k’ofa. Bayan sa tabi a hankali har suka shiga ciki, ba kowa daga su se masu aiki. A ranta tace wato kai baka iya cin abinci se kayi reserving, lallai kud’i ya maka yawa. A table daya zauna ta zauna itama, ko da waiter yazo d’aukan order’nsu Anas ne yamasa bayanin komi ita batace ko uffan ba ,wasa da siraran yatsunata kawai take tana kallon yankan da tayi shekaran jiya a yayinda Anas ke latse laste kan wayar sa. Bayan 3 minutes abincin su ya iso sede taga combination na yau yafi na ranan yawa, ba abinda babu kan plate nata k’wai ne kaza ne, kayan ciki na, pepper soup ne bade abinda babu shiko Anas kalan abincin ranan ya sake ordering. Toh mesa? Mesa za’a bani wannan babban plate cike da abincin kusan dubu biyar? Na Mr. Fauzi kuma na N1,500? Kode waiter’n yayi b’atan kai ne? “Uhm Sir are you sure wannan shine abincin nawa?” Ta tambayi waiter’n a yayinda yake zuba mata drink. “Yes Miss your Boss asked me to bring it for you.” “Boss?” Ta nanata a ranta tare da juyawa ta kalli Anas. Sam yi yayi kamar bema san maganar da sukeyi ba yakai spoon bakinsa a hankali. Bayan waiter’n ya tafi still Fannah ta kasa tab’a abincin ta dan bata yarda ba har yanzu. Anas kuwa dalilin dayasa ya sai mata abincin dubu biyar yau shine akoi time da ya tab’a kai Amal asibiti da menstral cramp ya tab’a rik’eta bayan da likita ya dubata ya bata maguna seyake cewa Anas a tabbata tana cin abinci me kyau saboda asaran jinin jikinta da take in tana period same goes to Fannah, sesu samu suyi restoring energy’n jikinsu. Itama saboda bleeding da takeyi yazamo dole taci abinci me kyau dan lafiyarta sesa ya siyo mata wannan abinci me kyau kuma me tsada. Ganin batada niyyan chi yasa ya dakata tare da kallonta, “well? Bara ki chi bane? Kinsan ba jiranki zanyi in na gama bako?” Baki na rawa tace, “S... Sir yayi yawa. In kace ni zan biya bansan ya zan biya ba.” Kallo ya watsa mata “last time da mukazo ke kika biya? Kin cika surutu, mschw. In zakici fine in bara ki chi bama fine” ya cigaba da chin abincinsa. K’in ci tayi wane ita abincin dubu biyar. Miss Aleeyu eat! Ko sena sab’a miki zakici? Ko kici kokuma in muka koma office inciro miki 500 papers kiyi zaman giaransu” Ai a hankali ta d’aga spoon nata ta soma ci a hankali, ta tab’a nan ta tab’a can sosai abincin ya mata dad’i. Bata san lokacin data baje ta fara ci kamar ba gobe ba Anas dake satan kallonta se mamaki yake mutum gata ba k’iba amman se aukin chi. Duk uban girman plate nata sanda taci morethan half, data jita dam tukuna ta goge bakinta ta kora da juice. Kallonta yake cike da mamaki har yasa ta jin kunya. “Kin k’oshi ko a k’ara?” Kai ta kad’a masa cike da kunya da nufin a’a. Waiter yakira ya biya kud’in plates nasu sannan suka kama hanyan dawowa office. *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:51, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 3⃣9⃣ Zaman makoki sukayi cikin motar har sanda suka iso building d’in. Office nata ta wuce a sanyaye shima Anas d’in office nasa ya nufa bayan ya zauna kan kujerar sa ya soma tunanin abubuwan dasuke faruwa dashi lately. “Me had’i na da lafiyan Fannah da har zan tambayeta ya jiki? Me sa zan saya mata meal me kyau? What is wrong with me?” Duk yadda yayi ya kawar da tunanin Fannah ya gagara ga wani san shan coffeen ta daya keson yi, no matter how yau seya sha coffeen nan. Surrender kawai yayi daga k’arshe ya kirata kan tazo bayan minti d’aya ta shigo. “Yes Sir” ta fad’i kanta a sunkuye. “Make me coffee.” Kai ta d’ago tana kallon sa cike da mamaki ba shi yace baya buk’ata ba d’azu? Meya canza masa mind toh? “Bakiji meh nace bane?” “Naji” ta amsa sa a takaice nan ta nufa wajen coffee machine d’in ta fara had’awa. Daidai lokacin wayar Anas ya soma ruri, yana dubawa yaga Shettima ba tare da b’ata lokaci ba ya d’ag “hello maza?” “Ya Anas gani da Amal fa muna cikin elevator ma yanzu ta matsu wai seta ganka harda lunch ta kawo maka.” “Iyeh!” yayi exclaiming tare da zaro blue eyes nasa “Kana nufin kuna building d’in yanzu?” “Eh Ya Anas gamu nan.” Ding! Ya katse wayar. “Ya Shettima me na fad’awa Ya Anas toh?, suprise nefa.” Amal ta fad’i tana turo masa baki harda harara. “Allah sa supbeans ne ba suprice ba, kuma the next time kika sake harara na wallahi kwad’e ki zanyi da mari.” Can k’asa k’asa tace, “mugu kawai.” Seko ya jita, “me kika ce?” Ya tambayarta tare da matse hannunta cike da mugunta. K’ara ta saki “awchh! Nace kayi hak’uri.” Kallon ya mayar mata shima tare da sake mata hannun. Anas kuwa lokaci d’aya hankalinsa ya tashi, kawai yaji bayasan Shettima ya had’u da Fannah, tun kafin ya ganta ma yana masa tsiya bale ace yazo ya gansu su bibbiyu. Take ya mik’e ya nufa wajen Fannah tare da fincikota da hannu kad’an ya rage ruwan zafin be zube k’asa ba. k’ara ta saki. “Argh! Mr. Fauzi me haka? Kasake min hannu.” Hannu ya aza kan lips nasa “shush!” D’akinsa ya jata wanda tuni zuciyar ta ya soma bugu “ki zauna anan, don’t move or talk and karki fito kin jini ba?” “Mesa?” ta tambayesa. “Because I’m your Boss Miss Aleeyu, I’m telling you kika fito daga d’akin nan 500 pieces zakiyi correcting.” Jin 500 papers ta giad’a kai cikin tashin hankali. “Good” yace tare da rufo k’ofar, kamar su Shettima suna jiransa daidai lokacin shida Amal suka shigo gudu tayi, tayi hugging nasa. “My Angel yau kuma visit aka kawo min?” “Eh Ya Anas ranan kace yunwa na damunka a office shine na kawo maka lunch cikin lunch box.” “Awwn! My Angel thank you” peck ya manna mata a forehead. “Zanci zuwa anjima” ya fad’a mata tare da ajiye flask d’in kan table nasa. K’aramin tsuka Shettima yaja erin kallesu d’innan mana. Ignoring nasa Anas yayi ya tambayesa, “Shettima yau ba lectures ne?” “Eh babu ina cikin bacci na wannan fitinanniyar ‘yar taka ta tadani wai setazo.” “Ba ruwanka, be tab’a kiba aiko Angel?” “Wallahi Ya Anas ya zungure min kai da muka shiga mota a elevator kuma ya kama min hannu da zafi.” “Haka ya miki? Bari muje gida mu rama miki.” “Ya Anas zanyi fitsari” kafin Anas yayi magana takama hanyan d’akinsa inda ya rufe Fannah gashi besa lock ba k’ofar kawai ya ja, kaman aljani ya b’ullo gabanta. “A’a Angel bareyi ki shiga nan ba.” “Ya Anas ya matseni” ta fad’i tana mammatse k’afa tana bugawa. “Bari Shettima ya raka ki toilet a k’asa.” Shettima uban san jiki wai, “mesa Ya Anas? Bayan ga toilet anan yaushe zan kaita har k’asa? Barta ta shiga mana.” “Shettima! Ka kaita toilet a k’asa.” “Ai seka fad’amin me kake b’oye wa cikin d’akin.” Fannah dake zaune kan gado duk tana jinsu, se mamakin yadda Anas yake walwala cikin ‘yan uwansa take, ashe de yana wasa da dariya ko dashike ai da yazo gidansu ma yata murmumushin munafirci but wannan kuma na gaskiya ne. “Me zan b’oye ciki? Abeg ka akita k’asa hurry.” “Ya Anas kode mace kake b’oyewa cikin d’akin?” “Shettima zan b’ata maka rai wallahi, giara akeyi ciki saisa bareyi Amal ta shiga ba.” Ya fad’a confidently sekace ba k’arya yake ba. Fannah harda rufe baki tana dariya, wato ma giara akeyi gaskia Mr. Fauzi ya iya k’arya. “Muga giaran toh” Shettima yafad’i yana wani shu’umin murmushi. “Shettima k’aniyanka, kaji ba.” Amal da tun d’azu ta kalli Anas ta kalli Shettima tace da ihu; “Ya Anas let me in fitsari please.” “Yi hak’uri Angel, Shettima setayi a jikinta zaka kaita ne?” Kallon tsiya Shettima ya ma Anas ina irin nasan mace kake b’oyewa cikin d’akin kawai zan maka shiru ne. “Taho muje Amal” hannunsa ta kama sun juya zasu tafi kenan Fannah ta saki ihu “Arghhhh!!!” daga cikin d’akin kunya ne ya kama Anas kaman ya nitse k’asa. Shettima da Amal ‘yan gulma tuni suka juyo. “Ya Anas yanzu dagaske akoi mace cikin d’akin nan?” cewar Shettima ido waje. “Ya Anas wannan ba muryar Ya Fannah bane?” Amal ta tambaya. “Wani erin Fannah?” kuma ya fad’a baki na rawa. “Masu giaran ne maybe d’ayan ta fad’i a toilet d’inne.” “Toh mu shiga mu duba ta mana” Amal ta fad’i. “Angel ba kinajin fitsari ba kuje, I’ll handle this myself.” Wani ihun Fannah ta sake k’urmawa tana bubbuga k’ofar. “Ya Anas Fannah ce open the door plasse.” Cewar Amal tana matsowa kusa da k’ofan. “Ya Anas k’aryan ka fa ya k’are bud’e k’ofar kawai muga Fannan ko Amal?” “Mr. Fauzi please open the door, wayyo Allah.” cewar Fannah cike da rashin hankali. Ran Anas in yayi dubu be b’aci ba lallai Fannah tanasan mutuwa yau. A fusace ya bud’e k’ofar kamar fara tafito tana kakkab’e skirt nata da hijabi. Ko lura dasu Amal ba tayi ba sanda ta tabbatar eh ba kenkeson data ga na binta a d’akin tattare da ita, tana d’ago kai suka had’a ido hud’u da Shettima daya sakar mata da murmushi sosai taga kamanninsa da Mr. Fauzi. “Ya Fannah!” Amal ta fad’a tare da hugging nata. Hugging nata back Fannah tayi, “Amal dear ya kike?” “Lafiya Ya Fannah mesa Ya Anas ya rufeki cikin d’aki ko kin masa wani abu ne?” Anas dake watsa wa Fannah wani mugun kallo yace, “Angel banasan suratan banza Shettima ka kaita toilet d’in daga chan ku wuce gida.” “Rowanta ake mana ne Ya Anas? Amal dama wannan ce Fannan?” “Eh itace Ya Shettima ka ganta kyakkyawa ba.” “Shettima kasan zan sab’a maka koh?” Cewar Anas yana galla wa Shettima harara. Yi yayi kamar beji abinda Anas yace ba, “Ai sosai ma Amal, Fannah Hi” yace da ita. “Uhm Sannu Shettima” tace dashi tana murmushin jin kunya. Kamar kyaftawan ido Anas yaja hannun Shettima da Amal yayi waje dasu tare da rufo k’ofar sa. Amal se knocking takeyi ignoring nata yayi, da ita da Shettiman suka gaji da kansu suka tafi. Bayan ya iso office d’in ya watsa wa Fannah wata erin mumunar kallo, cikin ta taji ya rud’e a lokaci guda. “Kin d’au wasa nake ko? 500 d’innan zaki giara yau.” “Mr. Fauzi wallahi ba haka bane kenkeso ne yabiyoni na rasa daga ina yafito.” “K’arya kike, bawani kenkeso kede kawai kice kinasan su Shettima su ganki, sun gankin kuwa kinji dad’i ai yanzu.” “Mr. Fauzi wallahi ba haka bane kayi hak’uri please.” “Nak’i, barinyi ba.” Table nasa ya nufa yaciro 500 copies tare da ajiyewa kan table d’in “ungo ga pencils anan d’auka.” Bata ko motsa daga inda take ba. Kamar wacce zatayi kuka tace “Mr. Fauzi please, I’m sorry plea-” katse ta yayi “the next time nace kizo ki d’auka zanyi doubling.” A tsorace taje ta d’aga papers d’in da pencils guda biyu. “Good wuce ki zauna ina kallon ki har ki gama.” Bayan ta zauna ta soma giarawa a yayinda ya zauna kan kujerar sa shima kaman TV yana kallonta harda crossing arms da legs, chan ya ciro popcorn yana d’an chi yana kallonta yana me jin dad’i. Guda ishirin tayi ta d’ago kai ta kallesa taga shima ita yake kallo ko d’an kunya yaji ya kawar da kansan nan beyi ba. Gira d’aya ma ya d’aga mata erin se meh dan kin kamani ina kallonki d’innan. A sanyaye ta mayar da kallonta kan papers d’in ta cigaba ita kanta tasan barata iya k’arisawa ba tunanin me zatayi take, “kuka? A’a koda nayi kuka ba sparing d’ina zeyi ba” chan idea ya fad’o mata. Pencil d’in ta jefar a k’asa tare da yin watsi da papers d’in ta sauk’a har k’asa tana rik’e da cikinta. “Wayyo Allah Mami! Wayyo ciki na!” A rikice Anas ya jefar da popcorn nasan ya taso daga kan kujeran sa ya d’aga ta tare da zaunar da ita kan kujerar. “Sannu koh? Ina ke miki ciwo?” ya tambayeta cike da damuwa. “Ciki na, wayyo zan mutu.” “Sorry zauna anan bari inkira driver yazo ya kaiki asibiti.” Kai ta giad’a masa se wani “awshh” take tana matse cikinta duk kuma na k’arya. A rikice ya kira driver’nsa “Hello Moosa? Kabar duk abinda kakeyi kazo right away.” Ding! ya katse tare da dawowa wajen Fannah. Fannah harda hawayen k’arya. “Ni kawai akaini gida wajen Mami, wayyo ciki na!” “Okay bari yazo sannu.” “Sir papers d’infa? I’ll go home in k’arisa su in na samu sauk’i.” “Forget about them, bakida lafiya kibarsu kawai.” Fannah dad’i kenan, ji take kamar ta taka rengem. Ai bada dad’ewa ba Moosa ya iso da k’yar ta mik’e dan munafirci. “In kira azo a d’auke ki neh baraki iya tashi ba?” Kai ta kad’a masa kawai “ya d’auko min jaka na a office kawai. Wayyo ciki na!” “Okay toh, Moosa je office nata ka d’au mata jakarta.” “Wayyo ciki na!” ta gwada yunk’urin tsugunawa taro ta yayi “sorry yanzu Moosan ze dawo kikace bara kije asibiti ba?” Kai ta giad’a a wahalince “ni kawai akaini wajen Mami Argh!!” “Bari ya dawo sannu koh, Moosa hurry up mana!” ya kirasa a tsawace. Nan da nan ya dawo da jakar ta. “Oya walk her down kuma bawai nace ka tab’a ta bane do you get me?” “Yes Boss.” “Mis Aleeyu lets go.” A hankali ta soma bin bayansa tana taka k’afa kamar barata iya ba. “Get well” Anas yace mata bacan da k’arfi ba amman tajiyo sa, kai ta giad’a masa as an answer. Haka har k’ofar gidansu Moosa ya kawo ta, godiya ta masa yana jan mota ya fice ta b’alle da dariya. “Ai nan gaba abinda zan na maka kenan, dan mugunta yaushe zanyi zaman gyaran 500 papers. Oh ni! Fannah, dama bacci nakeji barin je in huta.” Tana shiga ciki taci karo da Mami dasu Afrah anci gayu sekace za’a gidan suna. “Fannah ya haka? Yau da wuri” Mami ta tambayeta tana daidaita wa Aiman rolling nata na abaya. “Banida lafiya ne shine Mr. Fauzi yasa a ka dawo dani.” Daga yadda take maganar ma Mami ta gano k’arya take. “Wato seda kika rantse baraki wuni a office bako Fannah?” “Mami kamar ya kuma na rantse?” Ta wani turo baki. “Banida lafiya ne fah ki kira ki tambayesa mana.” “Toh Allah sawak’e in dagaske kike, mu zamu fita unguwa inkuma zaki bimu toh.” Har ga Allah Fannah nasan binsu amman saboda kar Mami tasake ganewa k’arya ta ma Mr. Fauzi ta hak’ura. “A’a ni zan huta adawo lafiya. Kekuma Afrah kallon ya isa ko?” “Hmmm!” Taja numfashi cike da gatsine “Allah kawo sauk’i in ciwon gaske ne.” “Sekiyi da ali garu kuma yanzu”,tana kaiwa nan ta fice d’akinsu bayan da su Mami suka tafi taje tasamu Baba suka sha hira sosai shima bada jimawa ba ya d’an fita cikin unguwa dan strolling yarage Fannah kad’ai. Tana rigingine jikin gadon d’akinsu tana buga game dan takasa bacci. ***** Tun tafiyar Fannah Anas ya kasa samun sukuni, ya take yanzu? Ciwon cikin ya dena ne? “ANAS IBRAHIM FAUZI!!!” Ya kira sunansa. “Get a brain and stop all these, mesa nake damuwa da Fannah? Badan ina santa bane saboda PA ta ce lafiyarta as well as lafiyar duk masu min aiki ya shafeni sesa nake damuwa amman badan wani manufa bane right?” Ya tambayi kansa tare da giad’a kai as an answer. Wayarsa ya d’au tare da kiran Moosa. “Boss yanzu na ajiyeta.” “Are you sure? Har gaban gidansu?” “Yes Boss.” “Good” yace masa sannan ya katse. Se ya d’au wayarsa ze kira Fannah se girman kai ya hanasa. Yayi hakan kusan sau talatin but still ya kasa kiranta da k’yar d’in k’yar ya iya ya kira ta. Tana cikin game call d’in yashigo batare da b’ata lokaci ba ta d’aga. “Hello Mr. Fauzi.” Tace a hankali kan me lafiya. “Miss Aleeyu kinsha maganinki?” “Yes nasha.” ta amsa a takaice. “Good get well...” Se yayi shiru. “Soon” yace can k’asa k’asa. “Thank you” tace dashi daga nan ya katse wayar. Fannah de mamaki take har yanzu yadda Mr. Fauzi ya rikice gabad’aya daga ganin batada lafiya. Bata kawo komi a ran ta ba, a cewarta kawai yanada tausayi ne inyaga mutum baida lafiya. Shima Mr. Fauzi bada dad’ewa ba ya wula gida. Ummie da Amal sun fita unguwa, Abuu kuwa ya tafi office, Shettima kad’ai ke gida ya baje kan dining chair tare da aza d’ayan k’afansa kan table d’in yana wani kakkad’awa sekace alhajin gidan. Anas na ganinsa ya sunkuyar dakai tare da k’ara saurin tafiyarsa dan sarai yasan yau Shettima seya tak’ura sa da zancen Fannah. Aiko Shettima na ganinsa ya mik’e daga inda yake zaune. “Fannah sannu awww ashe Ya Anas ne sorry kasan d’azu na kirata muka gaisa na amshi lamabrta gun Amal.” Cak Anas dakeson ignoring nasa ya tsaya tare da kewayo wa yana kallon Shettima, ba komai inbanda zallan kishi tattare da shi. “Kayi meneh?” ya tambaye.sa “Nace na kirata mun gaisa” ya kuma nanata kansa. “Tana da kirki ni wallahi ma santa nake, daga ganinta kawai naji ta kwanta min a rai.” Ya k’are maganar da hannunsa dafe kan zuciyarsa yana wani murmushin soyayya. “Shettima kaji na rantse wallahi kafita daga harkan Fannah, kai yaushe ma ka fara karatun har kana tunanin soyayya, da bakinka zaka ajiye mace in ka auro?” “Toh meh? Ba love bane? Ni inasan Fannah gaskia gashi kuma na karanchi bame girman kai da san abin duniya bace.” “Shettima you do wanna die right? Wallahi ko ka fita harkan Fannah ko ni da kai mu sasanta.” Dariya sosai Shettima ya kwashe da harda rik’e ciki. Cike da mamaki Anas ke kallonsa. Sanda yayi me isarsa sannan ya d’ago kai har da hawaye. “Ya Anas wallahi rantsuwa ba kaffara kana son Fannah, ji kishi karara, akanta yanzu har zakayi fad’a da ni wanka ma kenan. Heheh LOL Mr. Fauzi you are in love.” Fuskarsa a sake yace, “sake fad’a inji.” “Mr. Fauzi you are in love” Shettima ya nanata kansa. Ajiye jakar laptop nasa yayi tare da ciro takalminsa d’aya ya nufa wajen Shettiima haka suka riga guje guje manya dasu cikin parlour basu hak’ura ba seda suka fasa wani had’ad’d’en flower vessel. “Dandan! Wallahi in Ummie tazo kaine bani ba” cewar Shettima da hannu a saman kai. Tsuka Anas yaja “mschww dama ni na sayo kuma 50k ne ba se a sake siyo wani ba. D’au tsintsiya ka share ni na wuce d’aki na.” “Toh Fannah I mean Anas, ni sunayen ku ma sirke min nake.” Anas bece dashi komi ba ya shige d’akinsa kawai dan inze biyewa Shettima har fad’a se sunyi. Uban neman tsokana ne da Shettima, be bar Amal bama waye ze bari toh? *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:51, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 3⃣2⃣ Bece da ita komai ba yabiya masu kud’in abincin, ahaka suka dawo cikin motar suka koma office, a lokacin azahar yayi. “Sir excuse me zanje inyi sallah.” Ba tare da ya kalle taba yace, “you have 5 minutes to do so, in kuma kika tsaya hira da Yusuf kikayi delaying d’ina you’ll answer to me.” Kai ta giad’a a hankali ta ajiye jakarta ta fice bayan ta idda sallah suka had’u da Yusuf hira yakeson janta dashi amman sauri take kar ta makara Mr. Fauzi ya samu abin magana kai. “Yusuf kayi hak’uri please, minti biyar Mr. Fauzi yabani ko second na k’ara ze ci mutunci na kabari in aka tashi zanzo musha labari har se sanda ka gaji.” “Toh Allah taimaka aiki as PA wa Mr. Fauzi kam seda hak’uri.” yace da ita yana tausaya mata, a haka ta koma office nasa,yana zaune kan kujera yayi focussing kan laptop dayake aiki akai kafin ta zauna yace taje ta had’a masa coffee bayan ta had’a tazo ta ajiye masa. “Kinga flasks biyu da suke can?” Ya nuna da yatsa. “Eh nagani” ta amsa a hankali. “Good ki cika min su da coffee.” Ido ta bud’e tana kallon ikon Allah yanzu dan tsiya har flask biyu? Ya kai ina? “Bakiji bane?” “Naji” ta amsa a takaice. “Good off you go.” Bayan ta isa wajen ta juyo tana kallonsa, shan coffeensa yake hankali kwance yana duban laptop tare da yin wasu ‘yan rubuce rubuce time to time “Sir ba d’an wani babban roba ko kwanon da zan had’a ciki se injuye cikin flasks d’in tunda dayawa zan had’a coffeen?” Ta tambayesa a nitse. “Babu kuma koda akoi ma ba barin ki zanyi kiyi amfani dashi ba ga cups nan kina had’awa ciki kina juye har ki cika.” Wannan wace erin mugunta ne kwata kwata cup d’in fa k’ananu ne erin teacups d’innan yaushe har zata cika wannan manyan flasks. “Sir hakan ze d’au lokaci ba gara naje kitchen na ari bowl ba.” “Bara kiyi ba, kinga banasan musu na fad’a miki stop breaking my rules in zaki had’a good in barakiyi ba kuma in kira Mami in sanar da ita kina min rashin kunya.” Chan k’asa k’asa tace, “ba se kanada lambarta ba.” Murmushi kad’an yayi, “haka kikace?” Wayarsa ya d’aga ya kai kan contact na Mami da yayi saving just d’azu data ajiye jakarta zuwa yin sallah. “Zo kiga” bayan ta k’ariso taga eh fah lambar Maminta ne to ya akayi ya samu? Ba tare da tace masa komi ba ta koma ta fara had’a coffeen cikin teacup d’in tana juyewa cikin babban flask d’in. Tayi hakan kusan sau goma amman data gwada jijjiga flask d’in taji har yanzu da saura cikansa ko rabi, gashi ko soma cika d’ayan ma batai ba haka kamar tayi kuka ta samu ta cike d’ayan da k’yar ta zauna dan ta huta. “Kin gama ne?” Ya tambayeta Kamar wacce bara tayi magana ba tace, “da saura d’ayan.” “Well? Me kike jira toh?” “Sir hannu na yagaji barin d’an huta please.” “Hutu?” Ya tambayeta yana murmushi. “Kin tab’a ganin inda aka huta a office? Get up ki cigaba we have thousand of things to attend to.” Haka kamar ta kashe kanta ta tashi ta soma cika d’ayan har tsayawa take tana mik’a hannunta Anas kuwa ganin haka dad’i yake masa nan gaba zata sake barin masa aiki ba tare da ta sanar dashi ba seya biya duka coffeen dayayi missing time da ta tafi. Tana gamawa ta koma zata zauna, kafin ta zaunan ya kirata fuskarta ta yamutsa kan kashi sannan ta nufa table nasa. “Ina details dana rubuta a hannun ki d’azu?” Jakarta ta koma ta ciro wayarta takai kan inda tayi saving sannan ta tura masa gabansa “gashi.” Kallon wayar nata ya tsaya yi sekace bashi ya d’auka ya copy number ciki d’azu ba. “Wannan shi kike kira da waya?” ya tambayeta. Sosai tambayarsa ya bata mamaki haka kuma ya bata haushi taga de wayarta bara a zagesa ba, tecno ce D7 ba abinda bayayi, duk abinda iphone 6s nasa da samsung galaxy 6 edge nasa dayake tak’ama dashi taga nata ma yanayi kawai de d’an cracks ne wanda basu fi uku akai ba. Amsa daidansa ta basa “shine, kuma naga ga details da kake buk’ata a kai.” Biro da paper ya mik’a mata “ungo copy it down for me banasan wannan fashasshen screen nakin ya tsaga min hannu.” Kallonsa tayi tare da kad’a kai kamin ta amsa ta yi copying masa neatly bayan data gama ta mik’a masa d’aga wa yayi yana kallo ya d’au batada clear and neat handwriting ne da seya samu abin magana kai se yaga kamar tafi sa iya rubutu ma dan haka ya gwada yin shiru amman shegen neman maganansa bare barsa ba. “I don’t think wannan wayan kin zena recieving calls da emails me kyau yakamata asan nayi.” “Sir nifa waya na ba abinda ba yayi, kuma naga ta nan nake answering calls naka da.” “Da kikace, ada dakike as my coffee maker yanzu kuma you are my PA abin kunya ne ma in shiga dake cikin jama’a da wannan abin da kike kira da waya.” Kasa rik’e bak’ak’en maganganunsa tayi yanzu kam, abin nasa yayi yawa. “Excuse me Mr. Fauzi just because ina aiki k’ark’ashin ka be baka izinin looking down on me ba, I’m not ashamed ko ina zan shiga da waya na tunda ba wani ne yasaya min ba ni na saya da kud’i na.” “Wannan kuma ke ya dama na fad’a miki cikin rules naki banasan ina fad’an abu kina fad’a kema ba, I’m your Boss duk abinda na fada koda ba haka bane dolen ki kiyarda in baki san me kalman respect ba kisani yau.” Telephone nakan table nasa ya ja tare da danna ‘yan lambobi akai “hello? Akoi iphone 6 gold ne a shop naku?” On the other side matar tace, “yes Sir akoi.” “Good akawo min guda d’aya yanzu the money will be delivered very soon.” “Okay Sir thank you.” Kallon sa Fannah ta tsaya yi iphone 6 ma waye? Inma wa ita ne toh ya kwantar da bokatin hankalinsa ba amsa zatayi ba, tecnon ta ya isheta. “Stop starring at me” yace da ita yana me cigaba da abinda yakeyi cikin laptop d’in. Bata ce masa komi ba takoma ta zauna shiru tana mamakin hali irin na Anas. Bayan kamar minti goma knock ya shigo daga k’ofar office nasan. “Get the door” yace da ita hankalinsa kan abinda yakeyi. A sanyaye ta mik’e ta bud’e mace tagani sanye da uniform da k'aramar shopping bag na tambarin AA communications a hannunta. Bayan ta gaishe da Fannah ta mik’a mata leather’n, amsa Fannah tayi ta kai wa Anas tare da ajiye masa kan table wani card ya ciro ya mik’a mata da nufin takai wa matar tana kai mata, ta amsa tayi godiya sannan ta fice, ciki Fannah ta dawo kafin ta zauna Anas ya kirata. A gaban table nasa ta tsaya a yayinda ya mik’o hannunsa da nufin ta ajiye masa abu kai. Itako bata gane me yakeso ba dan haka ta tambayesa “excuse me?” “Bani wayarki” ya fad’a a nitse. Zatayi magana ya tsawa ta mata “nace bani wayarki! Don’t let me repeat myself.” Tsabagen tsoro bata san sanda ta ajiye masa wayar a tafin hannu ba. Bayan wayar ya bud’e tare da ciro sim nata “Sir meh zaka min da sim card?” Ta tambayesa ko d’aga kansa beyi ya kalleta ba bale ya amsa ta, daman micro sim cikin wayar tatan, nan ya bud’e leather'n ya ciro sabuwar iphone 6 pil daga ciki ya sa sim d’in ciki wayarta kuwa ya jefa a dustbin kusa da shi. “Excuse me! Mr. Fauzi taya zaka jefar min da waya a dustbin da kud’i fa na saya in kai bakasan almubazaranci ba kyau ba toh ni nasani” wajen dustbin d’in ta nufa da nufin zaro wayarta karap ya d’aga ya kai d’ayn gefen. “Sir ka bani wayata.” Drawer’n dayake ajiye kad’an daga kud’ad’ensa ya bud’o tare da ciro bandir na naira d’ari ya ajiye kan table d’in “I’m sure wannan yayi kud’in wayarki. Take ita tare da sabon wayanki.” Bandir na d’arin ta d’aga “zanje in sake siyan sabon waya kalan nawa in chenji ya rage zan dawo maka dashi amman ni barin karb’i iphone naka ba bana buk’ata.” “Miss Aleeyu!” Ya kira sunanta a tsawace. “Kap building d’innan bame gaya min magana, bame crossing d’ina se ke. Ko a gida in nayi magana ba’a objecting d’ina saboda haka ki mayar da hankalin ki, I’m your Boss not your friend.” Yayi lecturing nata cikin tattausar murya. “Wannan yazama karo na farko nakuma k’arshe da zan miki magana ko in saki yin abu kimin musu. Ki d’au iphone d’in, I don’t care ko kin koma kin sake siyan kalan wancan abinda kike kira waya dashi all I know is da wannan wayar zamuna business dake, now take it.” Shiru tayi chan ta mik’a hannu ta d’aga da kwalin duka. “Good” yace tare da mik’ewa “follow me.” Ba musu ta mara bayansa still a floor na saman yakaita zuwa wata office a saman aka rubuta *MISS ALEEYU* ajikin kuwa aka rubuta *PERSONAL ASSISTANT* bayan ya bud’e k’ofar ya shiga still tana biye dashi office ne babba me kyan gaske da table na katakon zamani da kuma kujerun office guda biyu, kan table d’in laptop ne seda telephone, dasu fax and printing machine da cup cike da pencils da biro da sauran office equipments irinsu stepler, pin, glue, dade sauransu. Gefe guda kujerar cushion ne 3 seater dogo me kuma fad’in da za’a iya kwanciya akai se ‘yar k’aramar fridge dakuma dispenser se kuma split AC dakuma toilet a ciki. Sosai office d’in ya had’u ya kuma yima Fannah kyau dan se kallace-kallace take kamar zata karya wuyar ta. “Kallon ya isa haka ba sekin karya wuyarki ba” yace da ita cike da kunya ta daidaita kallonta gu d’aya. “Kin iya karatu ba sena fad’a miki ba, nan office naki ne as my personal assistant kamar yadda kika karanta rubuce a bakin k’ofar. Duk wani abinda zaki buk’ata akoi anan, ba kuma na baki office bane dan kisamu wajen yin bacci da hira da saurayin ki aiki ne yakwo ki nan, wancan telephone should stay on always, karki kuskura koda wasa kiyi disconnecting daga jikin plug na bangon saboda dashi zan na miki magana as well as other staffs, clear?” Kai ta giad’a “yes.” “Good saboda haka yanzu ba ruwanki da office d’ina fashe ni na kiraki, nima zan huta da kallo, for now ki biyo ni akwai aikin da zan baki ki fara dan nasan na barki anan ba abinda zaki amfana se bacci.” Ita tama soma sabuwa da bak’ak’en kalamunsa. Jakarta ta ajiye ta juya tabi bayansa bayan sun isa office nasa ya zauna ya d’ago blue eyes nasa yana kallonta “ina jotter’n ki?” “Yana d’ayan office d’in” ta amsa sa a takaice. “Okay office d’inne zena d’auka miki record d’in kokuma so kike kicemin ilimi yamiki yawa da duk abinda na fad’a miki zaki iya d’auka akai ba mistake.” Share abinda ya fad’a mata tayi tace, “barin je in d’auko” “Make it quick” ya amsata yana duban rolex agogon hannunsa bayan minti d’ai Fannah tadawo rik’e da biro da jotter. Tun kafin ta bud’o biron ya soma bata aiki “Kije file room acikin first cabinet akoi stack papers type A-D kiyi printing sekimin e-mailing, bayan haka ina buk’atar neat handwritten version nasu, avoid any mistake. Sekije 5th floor ki karb’a wasu papers a wajen Miss Suleiman kiyi typing nasu a computer kimin e-mailing, take note kowani paper seprate document ne, bayan kin gama typing nasu print them out ki mayar filing cabinet kiyi arranging. You can go now.” Hannun Fannah har b’ari yake dan yadda take rubutun da sauri duk wannan uban bayani da numfashi d’aya Anas yayi dan mugunta, magana yake sauri sauri saboda tayi missing wani abu dan ta buk’ace sa ya koma baya seya samu ya zageta yanzu. A sanyaye ta juya ta fice file room 3rd floor ta nufa kamar yadda ya mata kwatance taga a rubuce a sama 1st cabinet papers d’in ta tsakuro sunyi kusan d’ari har yaushe zatayi typing nasu har tayi e-mailing sannan ta zauna ta k’ara rubuta su da hannu? ai aiki ne babba why not kawai in tayi typing tayi printing ai duk d’aya ne. Bayan ta tattara papers d’in ta haura 5th floor ta amshi papers wajen Miss Suleiman ta haura sama inda office nata dana Mr. Fauzi suke. Office nasa ta soma wucewa dan masa bayani bayan tayi knocking yace, “come in” tana bud’e k’ofar yaga itane sarai yasan meya dawo da ita, so take ta nemi alfarman printing stack papers d’in ba seta rubuta su ba, da gangan dan mugunta daman ya buk’aci ta rubutan dan kawai yayi punishing nata. Bayan ta k’arisa gabansa ta daidaita muryarta ko ze d’an tausaya mata ya yarda da k’udurinta. “Sir naje na d’ibo stack papers d’in nace ko ze yuwu kawai nayi printing nasu bayan nayi typing d’in? Ma’ana ba sena rubuta ba.” “Miss Aleeyu nan office ne ba gidan hutu ba, yadda nace sekin rubuta sekin rubuta off you go.” “Sir but plea-” bata k’are maganar ba ya dakatar da ita “banasan musu just go nima in huta.” Daman tasan ba yarda zeyi ba juyawa tayi ta nufa office nata. Chan ta soma da typing stack papers d’in bayan tagama ta masa e-mailing duka sannan tayi printing papers data amso wajen Miss Suleiman ta sauk’a taje ta jerasu a filing cabinet sannan ta sake haurowa ta koma office nata batasan a wani shekara zata gama rubuta wannan uban papers da suka kai kusan d’ari ba. Guda 20 ta rubuta amman wani erin zogi hannun ta yake mata, kuka ne kawai batayi ba haka da k’yar tayi ta huta ta rubuta hamsin saura hamsin. Telephone dake kan table nata ne yasoma ruri tana kai dubanta taga CEO rubuce akai kamar barata d’aga ba kawai ta sa hannu tayi picking. “Yes Sir” tace masa. “Kin gama?” ya tambayeta “A’a Sir da saura papers d’in fa har d’ari ne.” “Good kicigaba da yi in kin gama seki kawo min akoi aiken da zakije min.” Kamar wacce zatayi kuka tace, “Sir please kabar aiken gobe wallahi nagaji please.” Murmushi yayi cike da mugunta “kin gaji? Ai bakiyi komi ba tukun hurry up nan da one hour ki tabbata kin gama.” Ding! Ya katse. Tsuka taja “mugu kawai.” *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:51, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 4⃣0⃣ Shettima na gama share wajen kamar yadda Anas ya umurcesa ya wuce d’akin Anas. Knocking yayi Anas naji yasan shine “Shettima kashigo d’akin nan zan sab’a maka.” “K’yal k’yal k’yal” Shettima ya shek’e da dariya kafin Anas ya tashi yasa lock a k’ofar inaaa har Shettima ya bud’e ya shiga. “Fita toh” Anas ya fad’i yana nuna masa k’ofa. “Ai wallahi ban fita se munyi magana.” Punch ya kai masa a saman hannu “ai dama maye ne kai seka cinye d’akin zan koma parlour ko guest room.” Vest nasa Shettima ya kama “please mana Ya Anas I’m serious we need to talk.” “Wai akan meh? Ha’ah!” Anas ya fad’i a fusace. “Akan Fannah, Fannan office naka.” “Me zakace a kanta? In ma so kake kace ina santa to wake up you are dreaming ni bana santa har yau banga macen da zance ina so ba, ba’a yita ba. Fine, are you okay now? Zan iya tafiya?” “Ya Anas kenan bakasan meh soyayya ba wallahi, kana feeling abu amman baka sani.” “Toh love expert seka je inda akeson jin bayaninka kamusu amman ni banaso, sake min shirt.” Jansa Shettima yayi da k’arfin gakse da vest nasa sanda ya fad’o kan gado. “Toh Ya Anas bari kaji, inhar kana experiencing wannan abubuwan da zan lisafo whenever kana *_TARE DA_* da Fannah to you are in love. Na farko;” Ya numfasa, “Duk lokacin da kuke tare zakaji kansan kata kallonta, you can’t take your eyes off her.” Shiru Anas yayi yana nazari kamar d’azu kawai yaji yanasan yana kallonta har da d’aukan popcorn yanaci yana kallon Fannah, kuma ko a meeting d’in d’azu yakasa dena kallonta. “Na biyu, zakaji ka damu da ita, the moment abu ya sameta you’ll just be there for her, zakaji kanasan kana protecting nata from kowani erin harm da zezo mata.” Nanma nazarin yake kamar d’azu da batada lafiya kawai yaji yanasan ya taimaka mata yayi protecting nata. “Na uku, za kana kishinta daga ka ga na miji na mata managa ko na tab’a ta sekaji kanasan kashe koma waye shi a lokacin.” Nazarin yake kamar ranar daya kira Yusuf yake ce masa suna tare da Fannah, dakuma yau da Moosa yayi yunk’urin tab’ata da kuma d’azu da Shettima yace masa yana san Fannah. “Na hud’u, du-” katse sa Anas yayi “banaso! banaso!” Kunnuwansa ya rufe da hannayensa yana kad’a kai “No! No! No! No! It can’t be! I can’t love Fannah. No! No! Shettima get out please.” “Ya Anas ina sanka ne saisa nake fad’a maka duk wad’annan abubuwa. Tunda har Allah ya bud’e maka zuciyar ka accept it, kana san Fannah there is no denying in that. Change your life Ya Anas now is the time, ka manta da pass naka and move on.” “No! No! Absolutely no just get out please, I need to think.” “As you say” yana kaiwa nan ya fice. Pillown dayake rungume dashi ya wullar sanda ya fasa wani had’adden flower vessel a d’akinsan. “I can’t fall in love, bangama mission dana fara na breaking zuqatan mata guda d’ari ba guda 50 nayi sauran rabi, I can’t fall in love. Bareyi Fannah kizo ki b’ata min plans ba, I have to send you farther away from me, bareyi in so ki ba, ni ba’a haifeni dan inyi soyayya ba an haifeni ne dan in d’au revenge, in kuma koya wa mata lesson a life. No way!” ***** _Washegari..._ 8:00AM yama Fannah a office for the first time, bata k’ara ba bata kuma rage ba. Knocking tayi bakin k’ofar office nasa. “Enter” yace hannunsa biyu rik’e k’ark’ashin hab’ansa da alama tunani yake tun d’azu. Yana ganinta se kawai yaji damuwansa sun soma gushewa, sanye take da pitch hijabin daya mugun mata kyau tare da amshe golden skin nata, besan sanda ya fara kallonta ba yakuma kasa hana kansa kallonta, shi yarasa me yake kallo ma wajen Fannah. Is not as if tana shirin batsa ne bale ace ko jikinta yake gani, kullum cikin hijabi take amman inya kafa blue eyes nasa kanta baya iya d’agasu. Bebar kallonta ba seda ta k’ariso gaban table nasa. “Good morning Mr. Fauzi” ta gaishesa, dan takaici ko amsa gaisuwan ma beyi ba, files na gabansa da Kacallah ya kawo masa jiya yaja ya soma signing, abinda ya kamata yayi tun a jiyan amman tunanin Fannah ya hana sa. Fannah kuwa ganin baida niyan amsa gaisuwarta ta bud’o side bag nata tare da ciro jotter’n ta “ga schedule naka na yau Sir, inda akoi abinda za’a giara let me know. Zan koma office d’ina.” Bece mata komai ba ganin haka ta juya har ta kai da bakin k’ofa ya kira sunanta a hankali “Miss Aleeyu.” Cak ta tsaya “kar ki tafi.” Ido ta zaro wurur wuru bambarak’wai tajiyo kalamun kamar ya kar ta tafi, a hankali ta juya “eh? Sir?” Ta tambayesa. Kansa sunkuye yana kallon files na gabansan yace, “kar ki tafi office naki yau sit here” a hankali kamar ba shi ba. Bata d’au maganar dawata manufa ba kuma yanzu, dan yadda ta karanchesa yau seta ga kamar yana cikin damuwa ne maybe a gida aka b’ata masa rai dande a office kam ba wanda ya isa. A sanyaye ta koma ciki ta zauna kan cushion tana wasa da yatsunta. A hankali ya d’ago blue eyes nasa yana kallonta koda idanunsu ya had’u beji kunya ba kallonta ya cigaba da yi, take ta kau da kanta. Tsikan jikinta har tashi suke dan yadda blue eyes na Anas suke kallonta. Da kallon ya isheta se kawai ta mik’e be ce da ita komai ba illa binta da kallo da yake, wajen coffee machine ta nufa ta had’a masa sannan ta kawo ta ajiye kusa dashi. “Sir it seems kamar yau wani abu na damunka take this, it might help.”,Ita Fannah acewarta tunda in ita batada lafiya yana nuna ya damu itama bari ta mayar masa da kulawan in return sede kamar yadda tace ba’a gane halin Anas. “Banaso!” yace da zafi. “Jeki zubar banaso!” Ya fad’a a tsawace dayasa ta firgita. Me tayi ne da Mr. Fauzi baya san coffeen ta yanzu? “Mik’o min bottle d’aya a fridge.” Shaye shaye again! Ita abinda bata so kenan, mesa Mr. Fauzi zena shaye shaye. “Mr. Fauzi shan abunnan baida amfani please kadena” “Bakida right na fad’a min abinda zanyi pass me a bottle.” Bata ko motsa ba “now!” Ya daka mata wani irin tsawa bata san lokacin da ta je ta d’auko masa ba. Hawaye take sosai, ganin ya bud’e bottle d’in kawai ta juya bayanta shima koda yakai baki seya kasa sha ya rasa dalili. “Damn it!” Ya fad’i a fusace tare da wurgi da kwalban tatas! Ya fashe a k’asa. A firgice Fannah ta juyo ganin kwalban ya fasa taji dad’i sosai a ranta. “Sir take the coffee please” d’agawa tayi daga kan table d’in ta mik’a masa kallon cup d’in yake yana nazarin ya karb’a ko kar ya karb’a. “Ka karb’a please.” Hannu ya sa ya amsa tare da kaiwa bakinsa, kurb’i daya yayi kawai seyaji duk damuwansa sun gushe, abinda ko giyansa ma be tab’a masa ba. Atleast in giyan ne seya d’au kamar minti uku daga baya ma yazo seya kusan minti goma saboda yadda jikinsa ya saba dashi. He really missed her coffee like crazy be cire daga bakinsa ba sanda ya kurb’d duka. “Should I make you another?” Ta tambayesa kai ya kad’a mata. Amsar cup d’in tayi taje ta ajiye kan fridge sannan ta kama hanyan fita. “Miss Aleeyu ina zakije?” Ya tambayeta cikin sanyin murya kamar bashi ya masifeta yanzu ba. “Zanje in d’auko mop ne daga janitor’s closet (inda ake ajiye tsintsiya, mop da sauran kayan share dotti) in yi mopping wajen chan.” “Leave it cleaners zasu yi taking care of wajen just don’t go.” Wai meke damun Mr. Fauzi ne yau? Mafarki yayi ne yake tsoron a barsa shi kad’ai ko meh? Dawowa tayi ta zauna kan kujera duk lokacin data d’aga ido se suyi ido hud’u da Mr. Fauzi kallonta yake ko kyafta ido baiyi. Bata kuma d’aga ido ba se chan, tana d’agawa kuwa taga har yayi bacci kan table d’in. Through out jiya beyi bacci ba as se tunanin abinda Shettima ya fad’a masa kan Fannah yake ga kuma a gida ya kwana bareyi yayi shaye shayensa ba. A hankali ta mik’e ta nufa wajen nasa biron dake hannunsa ta karb’e a hankali yadda barata ta dashi ba tare da arranging kan table nasan tasa komai in place kamar ranan yau ma taga littafin data soma karantawan. “Mr. Fauzi” ta kira sunansa. Bacci yake me k’arfi ko jinta beyi ba. “Mr. Fauzi da ka tashi kaje d’aki ka kwanta, kwanciya anan ze iya haddisa maka ciwon baya.” Nanma shiru be amsa taba. Hannu ta gwada waving a fuskarsa taga ko motsawa idanunsa basuyi ba alaman bacci yake me k’arfi kenan. Littafin ranan ta kuma cirowa takai kan page data tsaya ranan se b’ari take amman kaman aikin dole takasa ajiyewa karantawa ta soma dukda tasan yin hakan haramun ne. _From the day Ummimi left us, my family was turn apart. You made me your son a drunker. Why do you have to leave? Why must you choose another guy over your family? Why will you have to bring back Angel (Amal) 8 months after leaving? Exactly a day after birth. Why are women cruel? Ummimi I’ve loved you but not now again, I’ve cared for you but not now again. I will never set my eyes on you again, God bless Ummi for caring for us just as her own kids. I hate you! Don’t ever come back. I promise to avenge for my family and I for what you did to us on all women of your kind. I promise to cause heart break and attack to 100-200 women so they will feel exactly how it feels to be abondoned. Only these three women I promise not to hurt, Ummie, Amal and the girl from the other night._ Mamaki ne da tausayi ne yacika Fannah. Allah sarki Mr. Fauzi ashe ba laifinsa bane duk abinda yakeyi yau, laifin mahaifiyar sa ce, mesa to zata barsu? Ashe saisa yake san Amal kamar ya mutu saboda bata sha d’umin mahaifiya ba. Allah sarki, gaskia duk sun bata tausayi, su nasu ba tafiya Baba yayi ba rashin lafiya ne amman seji suke duk ba dad’i time da jikinsa yayi worse bale nasu suna ji suna gani mahaifiyarsu ta tafi ta barsu. So wannan ne dalilin dayasa bayan ko wani kwana uku-hudu yana breaking up da ‘yan mata ashe ramawa yake. Shine dalilin da yasa baya mutunta mata kona misqala zarratun, amma dukda haka da besa shaye shaye aciki ba, ba abinda shaye shayen ze masa in banda sake b’atar dashi da yayi hak’uri ya rungumi k’addara. Next page ta juya zata karanta a yayinda Anas yaja wani dogon numfashi hannunta na b’ari ta mayar ta ajiye se bugu zuciyarta yake. Dudum! dudum! Sede Anas ya ganta lokacin da take mayarwan amma be gane me take ajiye wa ba ko files ne ko littafi be sani ba dan daga bacci ya tashi. “Me kikeyi anan?” Ya tambayeta. “I... I.. I” tama kasa magana. “I’m sorry” tace daga k’arshe. Idanunsa ya sake mayarwa inda yaga tana ajiye abu seyaga diary’n sa wajen, take mood d’insa ya canza danko Shettima da Amal bai barinsu su karanta. “Diary na kika maranta?” Ya tambayeta daga jin muryarsa a san he is angry. Shiru tayi se b’ari take. “I’m talking to you!” Ya fad’a a tsawace. Bata san lokacin data fara hawaye ba. “Sir I’m sorry.” “How dare you! Ke bakisan ba kyau karantawa mutum sirrinsa bane?” Kuka harda me sauti take dan yadda yake magana a fusace a kuma tsawace. “Am talking to you! Mesa zaki karanta min diary?” “Sir I’m s.. So..” Bakin ta b’ari yake tama kasa magana. Ita kanta tasan itace da laifi batasan wani gulman yasata karanta masa diary ba, kodan halan ta damu dashi ne tadamu da shaye shayen da yakeyi, tana san ta gyara masa gurb’arcacciyar rayuwar dayake living zuwa daidaicacciyar hanya. Batasan taga Mr. Fauzi na shaye shaye musamman ma data karanto kad’an daga cikin sirrinsa. Kuka take sosai wanda har ya soma damun Anas. Sekace ba shi ba, in akoi me san ganin Fannah na kuka be wuce Anas ba amman banda yanzu, bayasan jin kukanta. Sekuma yaji ba dad’i mesa ya sata kuka? “Me aciki dan ta karanta diary na, maybe tausayi na fara bata and she wanted to help, the problem is banasan help nata banaso.” Handkerchief yaciro daga aljihunsa tare da mik’a mata. Kukan take bar yanzu ba makawa, “wipe off your tears” yace ba tare da ya kalleta ba. Amsa tayi a hankali tayi kamar yadda ya buk’ace ta sede har yanzu bata bar raira kukan ba. “For goodness sake kukan ya isa. You passed the line banasan ana min shisshigi kema kin sani.” “I’m sorry” tace a hankali. “Ya isa you can go.” Hak’uri ta sake basa sannan ta fice. “Huh!” Numfashi yasaki “God what is wrong with me? Koda Amal ce ta karanta min diary nasan zan mata worse than this, firing Fannah ya kamata inyi amman nakasa, koda banyi firing nata ba yakamata in bata punishment na intruding min datayi amman nakasa, se wai ma taban tausayi naji banasan kukanta. Naji wai ma nine da laifi dan sata kukan danayi. Oh God no! I’m not in love I’m not.” *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:51, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 4⃣1⃣ Haka har da aka tashi Anas be sake neman Fannah ba. So yake ya nisantar da kansa daga gareta as possible enough as he can, saboda ya soma ji kamar maganganun Shettima gaskia ne. Saboda when it comes to Fannah he is weak abubuwa dayawa take masa wanda yaci ace ya koreta koya hukunta ta amman seyaji bare iya mata komai ba. Yasoma yarda eh he is feeling something for Fannah amman ba love bane tausayi ne kawai, yana tausayawa mata sede ko daya tambayi kansa tausayin me take basa yakasa answering. Fannah is his weakness. Fannah kuwa dad’i taji da be sake nemanta ba dan da wannan kayan kunyan da tama kanta na masa shisshigi harda karance diary’nsa bata san da wani idan zata sake kallonsa ba. Ita abinda yafi bata mamaki ma shine yadda Anas yabata hanky wai ta goge hawayenta bayan abinda ta masa, shin meke damunsa yau? Ta d’au atake zeyi firing nata kokuma ya mata wani abu makamancin haka amman seyayi sab’anin abinda take expecting. He is acting wierd yau, bata tab’a ganinsa haka ba shida yake fad’in kukanta bai damunsa segashi yau bayasan ji. Hanky’n ta ninke tasa cikin jakarta sannan ta mik’e tare da rufo k’ofar ta dan ganin lokacin tashi yayi. Ta rufe k’ofar office nata ta juya kenan sega Anas shima yafito suna had’a ido tayi saurin kawar da kanta. Public elevator tabi a yayinda Anas ke binta da kallo so yake yace mata ta zo su shiga elevator’nsa amman kuma girman kansa bare bar sa ba, wai mesa ma yakesan su shiga elevator’n sa bayan abinda ta masa d’azu? Sanda ta b’ace sannan ya nufa nasa ya shiga shima, kafin ya sauk’o kuwa tuni Fannah ta k’ara mai. A d’an wani shago ta tsaya tare da yima family’nta d’an siyayyan kayan k’walama. Isarta gida keda wuya. Mutane biyun data gani tsaye cikin gidansu ne suka mugun razana ta. Ido wuru wuru ta zaro tare da dafe k’irjinta tana me salati a zuci. “Baffah Khaleel?! Ya Farouq?!” Kai tasoma kad’awa danko bata yarda da abinda idanunta suke gane mata ba. Mami dasu Afrah dake tsaye gefe guda suma fuskarsu d’auke yake da damuwa. “Mami dan Allah kice min basu bane, tell me idanu na wasa suke min.” “Fannah manyan gari wato har gidan TV ake nuna ki, ‘yan matan nawa fa duk sun girma sosai tunba Fannah surikata ba.” Cewar Ya Khaleel yana wani murmushin mugunta. “Kai Farouq baka ga matarka bane da baraka mata magana ba? Jeku gaisa mana.” Wani tantirin dariya ne a fuskar Farouq a yayinda ya soma takowa gaban Fannah. Baya tayi take ganin haka “Fannah mata ta ya haka kuma? Mijinki ne fa ni, bekamata kina min haka ba, matso mana mu gaisa.” Sosai Farouq ya sake girma yazama cikakken na miji yanzu kyansa ya sake fitowa, sede iskancin nan nasa daya saba har yanzu yana yi be bari ba. “No don’t touch me.” Kamar kyaftawan ido Mami tashigo tsakaninsu, “Ya Khaleel meh amfanin haka dan Allah? Nasan kai da d’anka kunfi k’arfin mu dan Allah kuyi hak’uri ku koma inda kuka fito. Fannah bata san Farouq Ya Khaleel kayi wa Allah ka hak’ura da kai da d’anka dan Allah.” “Maman Aiman kenan, in kinga mun koma Bama toh wallahi da Fannah ne. Wace karuwar ‘yarkun ma wacce ko martaba battada, dan ni da Farouq zamu rufa mata asiri zaku wani tsaya kuna mana tsiya yau shekarunta nawa takasa yin aure, ba d’a na mijin da ze amince ya auri Fannah inba Farouq ba.” “Baffah Khaleel dan Allah kayi hak’uri ka rufa min asiri banasan sake komawa Bama, banasan Ya Farouq ni na rungumi k’addara zan gama rayuwata duka ba aure dan Allah kar ka aura min Ya Farouq.” Fannah ta fad’i hawaye na gangarowa kan kumatun ta abin tausayi. Tajima bataji tashin hankali kamar na yau ba. Ta riga da ta ajiye past nata a gefe mesa su Baffah Khaleel zasu dawo su hargitsa mata komai?? “In baki son shi to shi yana sanki sakariya kawai, aure tsakaninki dashi kuma farillah ne nan da ‘yan watanni, gomma tun wuri ku fara shiri, karatu ne Farouq yayi. Yanada diploma’nsa dakuma aiki me albashin da ze iya rik’eki. Kinga ko wannan karan ke zakiyi kayan d’akinki tunda kema kinada aiki. Abinda ya kawo mu dama kenan, bayan biki zaki bi mijinki Bama ku fara zama acan, in qaninan ya tashi ku gaishesa. Farouq mu tafi.” “A’a Baba ni ba yanzu ba semun gaisa da matar tawa tukuna.” “Karka damu akoi gobe ai, gobe zaka dawo har girki seta maka tunda matar kace, mu tafi.” Nan suka fice. Kuka me k’arfi Fannah ta rushe da. Mami na bata hak’uri haka Afrah da Aiman ma. “Mami ni shikenan Ya Farouq zan aura? Duk inda mukaje se sun tsakuro mu. Mami dan Allah do something wallahi banasan Ya Farouq mugu ne, azzalimi banasan sa Mami.” Ta k’ara shigewa jikin Mami tana kuka me tsuma zuciya. “Yi shiru Habibti in shaa Allah baraki auri Farouq ba kamar yadda Allah ya k’wato ki kwanakin baya haka ma ze miki yanzu mu dage da addu’a kawai.” “Ya Fannah kiyi hak’uri zamu tayaki da addu’a” cewar Afrah cike da tausayi. Kuka sosai Fannah takeyi haka yadda taga rana taga dare ta kasa bacci. A ranan kowa hankalinsa tashe yake basu san kuma ina zasu sake zuwa ba, basu san ko in sun bar Maiduguri akoi inda zasuje Fannah tasamu aiki me kyau kamar na nan ba. Baba ya tausaya wa ‘yarsa sosai ba kuma abinda yafi bak’anta masa rai kamar in ya tuna ba abinda ze iyayi ya cheto ‘yarsa daga halaka. Dan auren Farouq halaka ne yaron da besan darajar mace ba ko kad’an, d’an giya d’an iska. Daga Fannah ta rufe ido seta soma mafarke mafarke ganin ba mahilicci se Allah ta tashi tayi alwala tariga nafilfilu har seda k’arfinta ya k’are sannan tayi zaman istighfaar. Da safe ta tashi tana shirin office sanyi sanyi kamar wacce k’wai ya fashe ma aciki duk Afrah na kallonta takasa koda ce mata uffan dan tausayi. Mami ce tashigo ta tarar da ita tana sa kaya bayan gaisuwa Mami ta tambayeta cike da tausayi “Fannah ba se kinje office ba yau ki huta” “Mami gomma inje saboda zama anan ba abinda ze haifar min inbanda bak’in ciki jiya Baffah Khaleel yace Ya Farouq ze dawo yau, bana san ganinsa Mami na gwammaci naje office.” “Toh shikenan Fannah Allah kare kicire damuwa daga ranki kinji? Muna nan muna kan miki addu’a.” “Nogode Mami ni na tafi.” “Allah kare” both Mami da Afrah suka mata sannan ta fice. 8:01AM daidai ya mata a office na Mr. Fauzi kanta sauk’e a k’asa ta gaishesa, sama sama ya amsa. Jakarta ta bud’o tare da ciro hand kerchief daya bata jiya ta ajiye kan table nasa. “Gashi, nagode.” D’gawa yayi ya sake mik’a mata “na baki keep it.” “But Sir-” katse ta yayi “I said keep it” yace a hankali. Amsa tayi tare da masa godiya ta mayar cikin jakar ta. Har yanzu basu had’a ido ba dan kanta a sunkuye yake. “Ina schedule d’ina na yau?” Ya tambayeta yana danne danne a laptop nasa. “I’m sorry bansamu na had’a ba excuse me yanzu zanje in had’a maka.” “Mesa? Me kikeyi tun jiya da baki had’a ba?” Ya tambayeta cike da tsiwa. “I’m sorry” tace nan ma bata d’aga kai ba sede daga yadda take maganar Anas ya gano wani abu na daminta ya tambayeta meneh kuma girman kansa bare barsa ba. Kallonta ya tsaya yi kusan na minti biyu amman sam bata gwada yunk’urin d’ago kai ba bale ya kalli cikin idanunta ma. “Miss Aleeyu” ya kira sunanta a hankali. “Yes Sir” ta amsa ba tare da ta d’ago kai ba. “Make me coffee” ya fad’i. A sanyaye ta juya ta nufa wajen machine d’in sede hankalinta ko kad’an baya jikinta tayi nisa tunanin abubuwan da suka faru jiya she actually can’t believe Baffah Khaleel da d’ansa Ya Farouq sun dawo suna san maida ita Bama da bata sake tsammani zata koma wataran ba. Bayan ta gama had’a jagual-gualenta ta juyo dan ba coffee ba sunan abinda ta had’a. D’an k’usa ne ya kama mata hijabi agarin cirewa tayi b’arin coffeen duka ya zube a k’asa cup d’in kuma ya fashe. Kid’imewa tayi a lokaci guda batasan lokacin da ta tsuguna ba dan tattarawa. “Don’t Miss Aleeyu karki ki tab’a” Anas yayi warning nata da ihu chak ta maida hannunta. “I’m sorry” ta fad’i hawaye na cikowa a idanta. “I’m sorry please” ta sake basa hak’uri. Toh kuma kukan meh? Ai be tab’a taba, bekuma mata masifa ba kodan d’an ihun dayayi dan kar ta tab’a glass d’inne ya sata kuka? Tasowa yayi daga mazauninsa ya nufo gabanta har yanzu tana tsugune “get up” yace mata. A hankali ta mik’e kanta sunkuye se hawaye takeyi side bag nata ya mik'a hannu yaja a hankali, batace masa komai ba, bud’ewa yayi ya ciro handkerchief daya batan “wipe off your tears” amsa tayi ta na gogewa sede the more tana gogewa the more kukan yake k’aruwa harda me sauti da k’yar ya zaunar da ita. Besan me ba se kawai yaji ya damu da ita bayasan ganin ta tana kuka. “Miss Aleeyu mesa kike kuka na miki wani abu neh?” ya tambayeta a hankali. Kai ta kad’a masa da nufin a’a tana me cigaba da kukan. “Toh mesa kike kuka? Sabida glass cup da kika fasa min ne? Don’t worry I have lots more.” Kukan take har yanzu ba makawa hasali se k’ara volume na kukan nata ma take. “Miss Aleeyu what is it?” Kai kawai take kad’a masa chan ma ta tashi ta ruga office nata a aguje kan table nata ta baje sekuka take shark’af shark’af abin tausayi. Anas nason bin bayanta amman girman kai irin nasa bare barsa ba. “For goodness sake what is wrong with me? Mesa nake damuwa da Fannah? She is not my responsibilily so let her be, duk abinda ke damun ta ita taji wajen.” Mik'ewa yayi tare da zama kan kujerar sa yana me cigaba da abinda yakeyi. Sede inaa mind nasa gabad’aya yana wajen Fannah. What if har yanzu kuka take? Me aka mata ko daga gida ne aka b’ata mata rai? Wayarsa ya d’ago dan kiran Mami se in ya soma shiga se ya katse haka ya kasa kirarta dan tambayen meke damun Fannah. Meeting dayake dashi ma yau shi kad’an sa yaje saboda yasan there will be no point yaje da Fannah tunda haka ta taho yau tana kuka. Shi kad’ansa yaje though shima duk hankalin sa na kan Fannah bayan da meeting d’in ya k’are as usual driver ya wuce dashi hotel dan cin abinci. Ga abincinsa a gabansa amman yakasa chi, dududu sau nawa suka chi abinci da Fannah amman yaji yau inba ita bare iya chi ba kuma bawai fa baya jin yunwa bane kawai seda ita ze iya chin abincin. Kacallah ya kira kan ya sanar da Fannah driver ze zo d’aukanta yanzu dan bayasan ya kirata da kansa ta raina sa, hakan kuwa akayi bayan 20minutes aka kawo Fannah hotel d’in tana shiga tagansa zaune dan bata masan nan za’a kawo ta ba ce mata kawai akayi Boss na nemanta. Idanunta sun kumbura sunyi ja dan kukan datasha a hankali ta k’arisa gaban table nasa ta tsaya ba tare da tace uffan ba. “Sit” yace mata hakan ko tayi bada jimawa yasa aka kawo mata abinci sak irin na jiya. Nan ma “eat” yace mata. “I’m not hungry” ta masa k’arya dan kuwa ko breakfast batayi ba yunwa takeji amman batada appetite na cin abincin saboda damuwar dake kanta kad’ai ya isheta. Spoon biyar yakai yaga ko yunk’urin tab’a abincin ta batayi ba. “Miss Aleeyu bakiya so ne akawo miki wani daban?” Kai ta kad’a masa. “Then why are you not eating?” “Sir I’m sorry bana jin yun-” bata k’are maganar ba cikinta yayi wani irin kuka. “Yes kinajin yunwa eat.” Nanma kai ta kad’a masa. “Kichi kokuma in baki 500 papers kiyi correcting nasu” ya gwada taorata ko dan haka zata chi. “Okay I’ll do it in muka isa office d’in.” Mamaki sosai amsarta ya basa itan da kullum take had’asa da Allah in ya bata aikin yau ita ke fad’in zatayi kai tsaye? Toh meke damun ta? “Miss Aleeyu meke faruwa? Meke damunki? Tell me.” Ya tambayeta cikin sanyin murya dan duk yashiga cikin damuwa ganin Fannah a damuwa.” “Babu Sir thanks for your concern, zan jiraka a waje in ka gama se mutafi in fara correcting papers d’in da wuri saboda in gama on time.” “Barakiyi correcting komi ba, I don’t mean it kawai kichi abincinki kinji? You are sick har yanzu zama da yunwa won’t help, eat.” A hankali ta d’aga spoon nata ta soma ci sede ba hab-hab kamar yadda ta saba ba. Anas ko da jimawa yagama cin nasa yayi zaman jiranta saba’anin yadda ya saba. Dududu quarter kawai taci tace ta k’oshi. “Are you sure?” Ya tambayeta kai ta gaid’a masa. Bayan ya biya kud’in suka fice. Shigarsu mota Anas yace da driver “ba office zamu wuce ba gidansu Miss Aleeyu zaka kaimu.” Cike da mamaki ta d’ago kai se yanzu suka had’a ido dashi tun had’uwansu yau. “Gidan mu kuma Sir? Mesa?” “Saboda inji meke damunki.” Yabata takaicaccen amsa. “No Sir please don’t ba abinda ke damuna kawai fad’a mukayi da Afrah” tanasa k’arya “Ban yarda ba” ya bata amsa yana duban agogon sa. “Sir I’m serious.” Ita tsoronta kar in sunje su had’u da Baffah Khaleel kamar yadda ya saba kiranta da karuwa ko karya ya kirata gaban Anas. “Sir please mu juya na bar wayana a office I need to get it.” ta masa k’arya ko ze canza mind nasa. Resting kansa yayi jikin kujerar “karki damu zansa Ahmad ya kawo miki.” “Sir-” hannu ya aza kan lips nasa “shhh! Banasan surutu dayawa.” Ahaka har suka iso gaban gidansu Fannah zuciyarta se bugun d’ari d’ari yake. Driver na parking Fannah ta fito da sauri dan duba ko su Baffah Khaleel suna gida takai da shiga k’ofar gidansu kenan kawai suka ci karo da Ya Farouq kafin tayi wani k’wak’waran motsi ya cafko ta da hannu daidai lokacin Anas yake fitowa daga motan shima, idanunsa basu tsaya ko ina ba se kan hannun Farouq rik’e dana Fannah se k’ok’arin k’wata take amman ta kasa. Wani erin mahaukacin kishi yaji ya bugesa inba wai kashe koma waye mutumin yayi ba yana ganin bare samu sukuni ba. A fusace ya k’ariso wajen. “Matata me haka dan na kama miki hannu? Ke wai bakiyi missing d’ina bane? Ko d’an shafaki bara ki bari inyi ba?” Cewar Farouq dawani shu’umin murmushi fal a fuskarsa. “Ya Farouq ka sake min hannu niba matar ka bace let me go” ta fad’i tana hawaye tare da k’ok’arin k’wace hannunta. “Ka sake mata hannu!” Anas ya fad’a cike da isa. Fannah da Farouq tare suka juya suna kallon Anas. “Waye kuma wannan baturen?” Farouq ya tambaya. “Mr. Fauzi please ka tafi, don’t involve yourself in here.” “Kinsan sa kenan” Farouq ya sake tambaya. “Bade shima saurayin ki bane kina kwana dashi, kinsan sana'a sa’a.” Anas be san lokacin daya kai wa Farouq naushi a fuska ba da zobobin azurfa a hannunsa. Take hancin Farouq ya fashe gefen bakinsa yasoma na d’igan jini. *© miemiebee* beeenovels.mywapblog com [12:52, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 4⃣2⃣ Baki Fannah ta bud’e tare da aza hannunta bibbiyu kai cike da mamaki da tsoro duka. Hannu Farouq yasa tare da tab’a inda yaji moisture a fuskarsa yana dubawa yaga jini ta hanci da bakin sa, “Kai! Ni ka fasawa baki? Dama nasha jin cewa ku turawa bakuda tarbiyya yau zan koya maka.” Hannu ya d’aga da k’arfin da Allah ya bashi shima ze kai wa Mr. Fauzi punch ai karap Anas ya kama hannun nasa tare da murd’awa cike mugunta ta bayansa. K’ara sosai Farouq ya saki dan azaba. Fannah duk ta rikice “Mr. Fauzi please ka sake sa ya isa please” ko saurarenta Anas beyi ba k’ara murd’a hannun nasa yayi a bayansa k’ara sosai Farouq ya sake saki dan azaba. “Repeat what you just said.” Anas yace dashi, daga yadda yake magana ma kad’ai za’a san ransa a b’ace yake, na bala’i ma kuwa. Duk zafin da Farouq ya keji be hanasa misbehaving ba. “K’arya nayi dan nace kuna kwana tare karuwarka ce” “You really want to die” Anas ya sake shi, kafin Farouq ya sake wani k’wararren motsi Anas ya sake kai masa punch a fuska fiye da yadda yayi d’azu sosai jini yake fita daga baki dakuma hancin Farouq. “Mr. Fauzi please ya isa dan Allah” Fannah ta fad’i duk a kid’ime idanta tuni suka cike da hawaye. “Kai ko kasan waye ni? Mijinta ne fa ni, aurenta zanyi banza da kai zakazo kana intruding. In ita karuwan kan bata fad’a maka yanzu ai kaji I’m her husband. Ke Fannah dan iskanci ya miki yawa kin kusa aure ma baraki fad’awa ‘yan iskan samarukan kin su hak’ura bako?” Hannu ya mik’a ze jata dan wanke ta da mari. Kamar a kyaftawan ido Anas yajata bayansa kamar ‘yar baby tare da rik’e hannun Farouq, rik’o kawai ya masa amman idan Farouq sanda ya cike da hawaye. D’ayan hannunsa ya d’aga ze sake kaiwa Farouq mumunar punch Fannah ta rik’e hannunsa da nata bibbiyu. Hawaye take sosai “Mr. Fauzi please ya isa kayi hak’uri ya isa please.” Hawayen da takeyi ne kawai ya hana Anas kaiwa Farouq punch da ze iya kwantar dashi a asibiti. Kwalan rigar Farouq ya chukumo. “In bakada manners na magana wa kamilallaiyar mace I will teach you some, the next time ka sake kwatanta Fannah da wad’annan munanan suna I assure you zakayi kwanan cell, pathetic fool kawai, idiotic bastard.” Sannan yayi wulli dashi har k’asa Farouq yayi landing, daidai lokacin Ya Khaleel ya yanko kwanan gidansu Fannah shi a dole yazo cin abincin ranan da surikarsa ta dafa masa kamar yadda yace jiya. Ai ganin his only son a k’asa ga kuma jini ko ta ina fuskarsa ya falfala da gudu yayi kan Farouq. “Farouq meya same ka? Wani d’an shegiyan ya maka wannan tsiyan, waye shi?” “Baba kafin ka kira wani da d’an shegiya make sure ka cire sunan d’anka daga number a list d’in. Nayi warning nasa but I think I have to warn you too, the next time ya sake shiga harkan Fannah bare kwana a garin Maiduguri qalau ba.” “Tohh sannu fa, sannu shugaban k’asan Nigeria. Toh kaine d’an shegiyan ba d’ana ba, kai har kanada da right da zaka hana Farouq shiga harkan Fannah ne? Ka tab’a jin inda aka shiga tsakanin mace da miji?” Fannah dake tsaye bayan Anas tace, “Baffah Khaleel Ya Farouq ba miji na bane.” “Ke karuwa rufa min baki.” Ran Anas in yayi dubu be b’aci ba, taku yayi yunk’urin yi zuwa gaban Ya Khaleel dan kai masa had’add’en punch shima, “how dare you call Fannah karuwa!” yace a yayinda Fannah ta rik’e rigansa dan hanasa aiwatar da abinda yayi niyyar yi. “Mr. Fauzi let them be please, ya isa ka tafi wannan problem d’ina na ne bansan na jaka ciki, please go.” Wayarsa ya ciro a fusace bayan an d’aga yace, “Hello send me 10 men, I mean 10 a unguwar Polo...” Nan ya masa kwatance. Baki na b’ari police d’in yace, “yy.yyyes Sir right away!” Aiko cikakken minti biyar da gama wayan Anas beyi ba sega motan polisawa guda biyu. Farouq harda rud’ewan ciki Ya Khaleel kuwa sanda ya saki fitsari a wando shi be d’au dagaske baturen yake ze kira polisawa ba, toh waye shi. “Take them both, kuje ku rufesu right away” ya fad’a a fusace. Farouq da baki ke jini yace, “wallahi kayi k’arya me mukayi da zakace aje a rufe mu?” Can k’asa k’asa Ya Khaleel yace, “kai kayi shiru se yanzu nagane waye wannan mutumin, ba bature bane shine wanda aka nunasa da Fannah ranan a BRTV wallahi babban mutum ne mu basa hak’uri in bahaka ba in aka rufemu me bailing namu se Allah.” “Mr. Fauzi ko? Dan Allah kayi hak’uri, wallahi misunderstanding aka samu anan my apologies please karka sa a rufe mu dan Allah. Farouq baraka basa hak’uri bane?” “Officer take them away banasan jin komai.” Nanne bakin Fannah ya bud’u. “Mr Fauzi please kayi hak’uri karka rufesu dukda cewar basuda kirki ‘yan uwana na ne, Ya Khaleel Baffah na ne Ya Farouq kuma cousin d’ina kayi hak’uri and set them free please.” “Miss Aleeyu why? Bakiji munanan sunan da suke kiranki dashi bane?” “Naji Sir just please set them free, please.” Ta fad’a idanta na cikowa da hawaye. “Officer let them be zaku iya tafiya sorry for the disturbance.” “Ba komai Mr. Fauzi muna da godiya” “Zuwa anjima zakuji alert thanks.” “Mungode sir, mungode sir” a haka suka ja motocinsu suka fice. “Miss Aleeyu kinasan in samusu retricting order from the law yadda barasu sake zuwa kusa dake ba? So they won’t disturb you in na bar nan?” “Sir thank you but karka damu in shaa Allah ba abinda zasu iya min you can go kadena b’ata lokacinka akaina please, thank you” “Call me in wad’annan foolish mutanen suka sake miki wani abu” ya k’are maganan yana ma Ya Khaleel da Farouq kallon banzaye cikin banzaye. Farouq zeyi magana Ya Khaleel ya taka masa k’afa dan haka yayi shiru. “Ki shiga ciki.”,Ba musu bale gardama ta shige ciki sanda ya tabbata ta shiga ya dawo da kallonsa kan like father like son yana nuna su da yatsa “kun ji na rantse in kukayi ma Fannah wani abu zaku k’are rayuwanku a jail, assholes.” Yana kaiwa nan yashige motarsa driver ya rufe yajasa suka fice. Se yanzu bakin Farouq ya bud’u. “Shege se meh? Wallahi kasani ka tab’o tsuliyar dodo, zancen kakeso.” “Kai Farouq ya isa saurayin nan babban mutum ne a garin nan ka rufa mana asiri muyi abinda ya kawo mu mukoma da Fannah Bama cikin kwanciyan hankali.” cewar Ya Khaleel. “Wallahi Baba be isa ba ya zubar min da jini ya kwana lafiya Allah kaimu gobe. A ina yake aiki kace?” “Wai meka isa kayi masa ne dawani fashasshen bakin ka da hancin ka, se uban kurin baki wai kana zuwa gym ji yadda kabari wancan Fauziya ne ko Fauzi ya maka tatas. Kona fad’a maka inda yake aiki me ka isa ka masa?† “Niko nasan me zan masa just tell me ina yake aiki?” “A Flames Enterprises shine CEO’n wajen naga sun sa a TV” “Good” Farouq yace tare da ficewa. Babansa na kiransa ko a kwalan rigarsa, Ya Khaleel kuwa shegen tsoro ne dashi sekace farar kura. So yake ya shiga cikin gidansu Fannah amman kuma yana tsoron abinda Mr. Fauzi ya fad’a masa. Dan haka ya nufa masauk’insu kawai. Anas kuwa isar sa gida ya wuce d’akinsa tare da sa lock ba tare da yace da kowa komi ba. Wani irin tausayin Fannah yaji ya kama sa, ba abinda yakeso yanzu kamar yayi protecting Fannah daga wannan shegun Baffan nata da d’ansa. Mesa zasu na kiranta da karuwa? Mesa zasu na kiran yarinya me tarbiyya kamar Fannah da karuwa? To kode ta tab’a yin hakan ne da a baya se Allah yamata shiriya? “No!” ya fad’a a fili no matter what Fannah batayi kalan wanda zata iya aikata abinda uncle nata yake fad’a ba. Ai inhar dagaske karuwan ce da bare so ya aura wa d’ansa ba k’azafi kawai suke mata, ayyah ashe shiyasa taketa kuka a office yau, shiyasa ko abinci ta kasa ci. “I will protect you Fannah no matter what.” Ya fad’a a fili. ***** _9:23PM_ Fannah da family’nta ne zaune d’akin Baba yanzu tagama basu labarin abinda ya faru d’azu, abinda Mr. Fauzi yama su Ya Khaleel. Kowa wajen yasha mamaki matuk’a. “Alhamdulillah! Alhamdulillah! Allah sak’a wa Anas da alhkairi, abinda yama Ya Khaleel daidai ne Allah saka masa da alkhai” “Ameen” kowa ya amsa wajen. “Habibiti amman har duka Anas yama Farouq?” Mami ta tambaya cike da mamaki. “Eh Mami, Mami tsoro nakeji wallahi Ya Farouq ze iya cewa ze rama dukan akaina.” Rungumota Mami tayi gam ajikinta tana shafa jelar gashinta da d’ankwalinta be samu ya rufe ba. “In shaa Allah ba abinda ze miki kina da Allah bayan haka kuma ga Anas na tabbata bare bari wannan shegen Farouq d’in ya miki wani abu ba.” ***** _10:30PM_ “Wai ina wannan hegen yaron yajene?” Cewar Ya Khaleel da kansa for the 100th time yana duban k’ofar one room apartment da suka d’an kama da d’ansa. Chan ya hango shadow’n mutum, torchin hannun sa ya haska, ganin Farouq ke tahowa ya saki hamdala tare da nufan wajensa. “Kai Farouq ina kashiga tun d’azu? Kasan na rasa mahaifiyarka barin iya juran rasaka ba kaima. Kuma dan rashin hankali haka kata yawo a gari da fashasshen baki da hanci?” K’eyarsa ya tand’e “wuce ciki mu goge maka.” _5 minutes later..._ Farouq ne mik’e kan ‘yar katifarsu a yayinda Ya Khaleel ke treating masa ciwon da Anas yaji masa a fuska da dettol. “Ina kaje ina tambayarka tun d’azu kamin shiru.” “Kai de Baba Allah kaimu gobe se Mr. Fauzi ne ko Fauziyan nan ya raina wa kansa nan gaba ko kafad’an juna muka buga bare min koda kallon banza ba.” “Wai me kake nufi Farouq? Kaga fa ka rufa mana asiri ni na fad’a maka kokuma in anzo tafiya damu in ce mai kai kad’ai ne banda ni, am warning you.” Lebb’an sa yacize irin mazan nan mana aikuwa yacize wajen ciwon. ★★★ _Washegari..._ K’arfe 8:10AM ya ma Fannah a office na Mr. Fauzi tun 8:00AM yake jiranta a zatonsa ma ko barata samu zuwa ba se kawai ya ganta, har cikin ransa yaji sanyi sede yau ma fuskarta ba walwala kamar jiya. As usual ta k’ariso gaban table nasa ta gaishe sa kanta a sunkuye. “Good morning Mr. Fauzi.” “How are you feeling?” ya tanbayeta a hankali. “Alhamdulillah, thank you for yestarday.” “Ba komai” yace mata. “Sir bansamu nayi making schedule naka jiya ba am sorry.” “Is okay” yace mata ba tare da ya nuna damuwa ba. “Mesa baki fad’a min ba?” Ya tambayeta. A hankali ta d’ago kanta idanunsu na had’uwa ta sake sunkuyar da kanta, “I’m sorry” tace sincerely. “Baki amsa min tambaya na ba, mesa baki fad’a min abinda wad’ancan biyun suke miki ba. Saisa kikazo jiya kika ta kuka kenan koh? Akansu ne?” Kai ta giad’a a hankali. “Mesa baki sanar dani ba?” “Sir I thought there will be no point in fad’a maka sesa kawai nayi shiru.” “Next time call me up and tell me kinji?” Kai ta giad’a tare da godiya. “Sun sake miki wani abu?” “A’a.” “Dagaske ne zaki auri wancan Farouq d’in?” Ya tambayeta kamar me jin kishin ta. Kai ta giad’a a hankali. “Mesa? Kina son shi ne?” Nanma kai ta giad’a. “Miss Aleeyu” ya kira sunanta “na’am” ta amsa kan ta a sunkuye. “Look at me.” A hankali ta d’ago kanta tana kallonsa kamar yadda shima yake kallon nata. Ba komi ne tattare da idanunta ba inbanda tsoro. “Do you really love him?” Ya sake tambayar ta cikin sanyin murya. Hawaye tajiyo na ciko mata, “no Mr. Fauzi banasan sa, ban tab’a san sa ba, mugu ne, azzalimin da besan daraja ta ba.” “Shhh is okay kar kiyi kuka, bakiya sansa baraki aure sa ba kinji?” Har hawayen nata sun soma sauk’owa ya ciro hanky ya mik’a mata amsa tayi ta share hawayen. “Sir how? Baffah Khaleel is powerful ni nasan dole zan auri Ya Farouq.” “No baraki aure sa ba I promise, jeki huta Kacallah ze kula da aiki ki yau.” “Sir don’t worry zan iya yin aik-” bata k’are maganar ba ya katse ta “banasan musu idanunki sun riga sun nuna baki samu bacci ba jiya so just go before I change my mind.” A hankali ta juya sanda takai bakin k’ofa sannan ta juyo tana kallonsa taga yana tattara files na gabansa “Mr. Fauzi” ta kira sunansa chak ya bar abinda yakeyi tare da d’ago blue eyes nasa yana kallonta. “Yes?” Ya bata amsa. “Thank you” tace dashi. D’an murmushi ya saki wanda ya sake bayyano da kyan sa. Giad’a mata kai yayi as an answer sannan ya cigaba da abinda yake a yayinda tafice zuwa office nata ita kuwa. Batasan me ba amman kwana biyun nan in *_TANA TARE DA_* Mr. Fauzi setaji she is safe kuma setaji ta ba damuwa. Kan cushion nata ta baje a hankali bacci me uban nauyin gaske ya isketa wanda takasa yi jiya da daddare dan yadda damuwa suka mata yawa. _30 minutes later..._ A nitse kuma a hankali Anas ya bud’e office na Fannah. Taku d’ai d’ai yake a hankali har yashigo cikin office d’in zube ya sameta kan 3 seater tana bacci peacefully. Har gabanta ya tako tare da tsugunawa d’an hijabin daya tare mata fuska yasa hannu ya gyara dogayen eyelashes nata yatsaya yana kallo sannan yakoma kan girarta dayake nan kamar na Kajol na india yadda ya had’e me kyan bala’i. Sekuma d’an siririn hancinta dayake nan madaidaici dakuma d’an bakinta dakenan ba k’aramin chanba bakuma babba ba tsakatsakiya. Besan dalili ba amman kawai ya tsinci kansa cikin jin dad’i, killer murmushi ne kwance kan kyakkyawar fuskarsa wanda ya lotsar da dimple nasa na gefe d’aya. Jakanta dake saqale a kafad’arta ya zira hannu ya cire a hankali yadda bare tada ita ba, tare da ajiye wa a gefe guda, k’afafunta ya daidaita kan kujerar tare da kunna AC’n a medium ta yadda beyi yawa ba bekuma yi kad’an ba. Ficewa yayi zuwa d’akinsa ya d’au wani arabian bargonsa me uban laushi da pillow yazo ya rufeta dashi tare da aza kanta kan pillow’n ya juya ze fita kenan Fannah ta kama bakin suit nasa ta baya chak ya tsaya tare da juyowa hannun nata ya raba da kayansa a hankali sannan ya rufo mata k’ofar ya fice zuwa office nasa. Yau yagama had’a model nasa sauran asalin gini yanzu. Already filinsa na nan kawai abinda yarage shine asa drawing d’in into action. *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:53, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 4⃣4⃣ “Miss Aleeyu barin je ba kema leave I can take care of myself” hannu ya mik’a ze amsa pillow’n se kawai ya saki k’ara dan zafin dayaji a cikinsa saboda blows da Farouq ya riga kai masa. A rikice tace, “meneh Mr. Fauzi?” Kafin ya amsata ya mata k’arya ta kwaye bedsheet d’in daya ruhu dashin, hannu ta aza kan bakinta cike da mamaki “Subhanallahi Mr. Fauzi dan Allah meya sameka? Ina kasamu wannan ciwuka? Kalli cikin ka? Ya Salam!!!” Ta fad’i tana hawaye tana kallon cikin Anas da yayi har wani purple brownish colour dan azaba. “Mr. Fauzi meya same ka please?” Ta sake tambaya hankali tashe. “Nace miki babu in kinsan kuka zaki tayi anan kuma go, leave, I can take care of myself.” Innalillahi! what do I do now ta tambayi kanta barata iya barin Anas haka ba he is badly wounded ga fuska ga ciki meya samesa ko b’arayi ne suka shigo suka masa duka? Amman kuma ai gidan tsaf yake ba abinda aka b’arnata. Toh meneh? “Mr. Fauzi please kayi hak’uri mu kaika asibiti kaji? Yi hak’uri.” Ta fad’a still tana hawaye dan tsantsan tausayi. Danko ba wanda zega ta’addancin da aka ma Anas be tausayawa masa ko be zubda hawaye ba. “Nace miki barinje ba kitafi please.” Wayarta ta ciro zata soma dialing number’n Amal dan sanar da ita halin da ake ciki. “Me zakiyi?” ya tambayeta. “Zan kira Amal ne in sanar da family’nka I’ve found you tun jiya suke neman ka.” “No karki kira su hang up.” “But Sir-” katse ta yayi ta hanyan daka mata tsawan da seda shi kansa ya masa ciwo “I said hang up!” Kansa ya dafe yana muntsika fuska cike da azaba. Nan ta katse ta matso kusa dashi “Sir kanka ke ciwo?” Niyan shareta yayi da farko sekuma ya giad’a mata kai a k’arshe. Jakarta ta ajiye kan side drawer ta nufa toilet tare da fitowa da bowl cike da warm water data d’iga dettol ciki dakuma towels guda biyu, jakarta ta ture gefe tare da ajiye bowl d’in akai. Kallonta yake “me zakiyi?” “Sir your face is a mess, zan goge maka ne.” “Banaso just leave.” “No Sir I’m not leaving mesa kai zaka taimaka min amman ni bakasan na taimaka maka? Saboda bankai inyi offering maka help bane? Saboda ka raina ni banida standard? Saboda ni talaka ce? Is that it Sir?” “No Miss Aleeyu that is not my point...” sekuma yayi shiru. “Toh kabari in biyaka taimakon dakake min koda na yau ne.” Shiru yayi chan ya giad’a mata kai. A ranta tace, Ya Allah kar ka kamani da laifi saboda zan tab’a na mijin da ba muharrami na ba, baida lafiya ne taimako zan masa, astaghfirullah. Nan ta tsoma d’ayan towel d’in cikin ruwan d’umin tare da matsewa a hankali ta d’an tab’a gefen bakinsa daya fashe. Towel d’in na tab’a wajen yajiyo zafi sosai hannunta ya kama “Sir nasan zeyi zafi hak’uri zakayi kaji? Sorry” a hankali ya sake hannun nata. Tana sake tab’a wani waje ya saki k’ara “arghhh! Ya isa kibari ze warke da kansa, go home” “Mr. Fauzi please mana kabari koda germs d’inne a kashe tunda baraka je asibiti ba. Please” Haka a nitse cike da tausayi ta riga bin duk ciwon da ke kan fuskarsa tana gogewa a hankali, sosai Anas ya riga sakin k’aran azaba in towel d’in ya tab’a masa kan ciwon ita kuwa duk lokacin daya yi d’an ihu seta basa hak’uri. Tagama da fuskarsa sauran cikin. D’ayan tsumman ta d’aga ta sa cikin ruwan kamar yadda tayi d’azu bedsheet daya rufe jikinsa dashi tasa hannu ta kwaye zuwa cibiyar sa. “Me kuma zakimin?” Ya tambaya yana k’ok’arin jan bedsheet din gam ta rik’e tana me hanasa yin hakan. “Ba abinda zan maka Sir zan d’an matse maka wajen ciwon ne.” “Don’t worry ze warke da kansa. Wai ke bakia jin tsoron zama da namiji kad’ai ne under thesame roof?” ya gwada tsorata ta ko zatace ta hak’ura zata tafi. “Ina ji amman in da kaine bana ji, I trust you Mr. Fauzi nasan ba abinda zaka min shiyasa. Yi hak’uri in d’an matse maka cikin kaji?” sanda ya k’are mata kallo sannan ya giad’a kai. A hankali ta aza hannunta kan cikinsa ta matse towel d’in kai. K’ara ya saki sosai dan azaba tare da rik’o hannunta. “Awwchh! Kibari ya isa ze warke da kansa, arghhh!” “Sir hak’uri zakayi sauran kad’an sorry.” Haka tata lalashinsa kamar d’an yaro. Towel tasake canzowa tare da k’aro ruwan zafi kan ruwan dan ya riga ya huce. Bayan ta zauna ta sake tsoma towel d’in ciki, cikin siririyar muryarta tace, “Sir did you get drunk yestarday” Shiru yayi kamar be jita ba. “Sir?” Ta kirasa. “No” ya mata k’arya danko besan taga kwalban a bakin k’ofa ba. “Toh wancan fa kwalban meh?” Ta tambayesa a nitse. Kai ya d’aga yaga kwalban sekuma yaji kunya. “Toh me ruwanki dan nasha? You are not my mother ko ita mahaifiyar tawa bata isa ta hana niba, stay out of my personal li-” be k’arisa fad’in ‘life’ ba yasaki ihu “arghh!” Sanadiyar tab’a masa kan inda ke masa zafi sosai da Fannah tayi. “I’m sorry” tace “sauran kad’an.” Chan ta nisanta, “Mr. Fauzi will you listen to me in na fad’a maka wani abu?” Kamar wanda bare ce komai ba seyace “meh abun?” Sanda ta sake matse towel d’in ta mayar kan cikinsa tana daddanewa kan ciwon a hankali tace, “if I were you, in za’a maidani kai abani kyanka da kud’inka da ilimi da komai da kake dashi I will thank God barin na wasting rayuwa na akan shaye shaye ba. Masu shaye shaye sune wanda basuda aikin yi, wanda basuda ilimi basuda komai se shaye shayen da sukeyin. Amman kaga kai komai Allah ya baka Mr. Fauzi, you are handsome, rich and very intelligent, me kake nema? Don’t you think bakayi adalci wa Allah ba ta hanyar masa godiya da shaye shayen da kakeyi?” A hankali ta d’ago idanunta tana kallonsa shima kallon nata yake da blue eyes nasa sannan ya kawar da kallonsa daga gareta. “Kayi shiru Mr. Fauzi, do you think you are fair to Allah? Bayan ya gama baka komai seka gode masa ta hanyar bijire wa dokokinsa na hana kowane muslimi shaye shaye” “No I’m not” ya fad’a ransa b’ace, muryarsa cike da weakness. “Ke bakisan mesa na mayar da drinking abinyi ba kidena intruding min cikin personal life. Get up and leave” yace a lokacin daya d’aga hannunta daga kan cikinsa. “Yafi ace ka rasa mahaifiyar ka ko mahaifinka kokuma d’aya daga cikinsu ya gudu ya barku? Is that the reason kake shaye shaye?” Kallonta yake totally speechless chan kuma ya tuna ashe ranan ta karanta masa diary, cikin chan tagani. Hannunta ta raba da nasa ta mayar kan cikin nasa. Hannun nata ya kuma d’aga daga kan cikinsa “ya isa you can go banasan maganan nan, saboda kin karanta min diary hakan be baki daman fad’a min whats right or wrong ba. I’m still your Boss” “I know Mr. Fauzi, you are my Boss. Ammana in saboda mahaifiyar ka kake misleading precious rayuwarka ta hanyar shaye shaye you are destroying your bright future. Hakan na nuna you are weak yana nufin ka barta taci nasara kanka kenan. Show her you are strong ko ba ita you can live your life, ka mance da ita and move on if possible forgive her if not ka mance da ita. You have a very bright future kadena b’atawa ta hanyan shaye shaye kaji Mr. Fauzi?” Shiru yayi bece komai ba as ya wula cikin duniyar tunani yana nazarin duk abinda Fannah ta fad’a masa. Tabbas ba k’arya ko d’aya cikin abinda ta fad’a masa dan kuwa haka Shettima ma kullum ke fad’i masa sede koda Shettima ya masa magana bai san sauraro amman yau da Fannah tamasa maganar seyaji yanasan yayi moving on ya manta da abinda Ummimi ta masa sede bawai ze yarda ko ya aminta da mace bane a rayuwarsa ever again he is already broken. “Can you do that Mr. Fauzi for Amal’s sake?” Kai ya kad’a mata da nufin “a’a.” “For mahaifinka?” Nanma ya girgiza kai. “Ummie?” girgiza kai still yayi. “For Shettima?” Nan ma haka. Cike da kunya tace, “for me?” Jiran masifar sa take setaji yace, “yes” a hankali sounding defeated. Idanunta ne suka sake bud’uwa cike da jin dad’i da murna. “Dagaske Sir? Zaka dena shaye shaye and move on?” “Yes” ya sake fad’i. Dad’i taji sosai wanda ta kasa b’oyewa. “You promise Sir?” ta tambaya dan sake tabbatawa. “I promise” yace. Sede duk maganan nan da suke baya kallonta. “Look at me please Sir” tace cikin murya me dad’in sauraro. Yi yayi kamar be jita ba. “Please” ta rok’esa a hankali ya dawo da blue eyes nasa kanta. “Da gaske baraka sake tab’a giya ba?” Ta tambayesa suna kallon juna. Kai ya giad’a a hankali “I promise.” “Mr. Fauzi thank you, thank you so much nakega am the happiest woman on earth yanzu, tun ba yau ba nake addu’ar Allah nuna min rananda zaka dena shaye shaye se gashi Allah ya nuna min yau, thank you so much.” bece me komai ba. Nan da nan ta gama matse masa cikin yadawo clean ba jini ko d’igo d’aya jikinsa sede zafin da yakeji. Tashi tayi zata toilet ta zubar da ruwan Anas ya rik’o hannunta a hankali takai dubanta kan hannun nasa sannan kuma zuwa kan Anas d’in tanasan tace masa ya sake mata hannu amman kuma tana tsoro kar yace ze canza mind nasa batun shaye shayen da yace ya dena. Godiya yakeson mata amman girman kansa ya hanasa, seya bud’e baki zeyi magana se wani abu ya tsaida shi. Da k’yar ya iya ya sauk'e girman kan yace; “Thank you.” ya fad’i a hankali ko kallonta baiyi. For the first time daya soma mata godiya kenan. Ita kanta abin ya bata mamaki, yau Mr. Fauzi ne yake mata godiya?! “You’re welcome Sir” ta amsa sa a takaice da murna fal a ranta. Hannun nata ya sake ta fice zuwa toilet bayan ta fito ta zauna bakin gadon kamar d’azu “sir kayi sallan Asuba?” K’arya yakeson mata yace ‘eh’ sekuma yaga ba amfani tunda ta riga tasan kad’an daga cikin sirrinsa. Kai ya girgiza mata. Kawai se jikinta ya bata ko isha ma beyi ba. “Isha fa?” ta tambayesa a hankali cikin dabara yadda bare fusata ba. Nan ma girgiza kai yayi. “Toh Maghrib da La’asar fah?” Can k’asa k’asa yace, “nayi la’asar.” “Masha Allah its not too late, barin had’a maka warm water sekayi wanka dan jin dad’in jikinka sekuma kayi yi alwala ka rama sallolin da ake binka koh?” Haka kawai ya tsinta kansa cikin san cika wa Fannah qudiri dakuma burinta. Kai ya giad’a mata. Nan ta mik’e cikin minti biyu ta had’a ta dawo. “Sir ina bath towel naka?” Nuni ya mata da hannu wajen ta nufa ta ciro “gashi” ta mik’a masa zan jira ka a parlour tana kaiwa nan ta fice. Sanda yayi dagaske sannan ya samu ya miqe daga kan gadon, bayi ya fad’a. Shigansa bayi da minti d’aya Fannah ta dawo ta nemi sallaya ta shimfid’a masa bayan tayi amfani da wayarta ta gano Qibla. Nan ta fice, kitchen nasa ta nufa ta d’anyi dube dube sede bataga abinda zata dafa masa ba. Fridge nasa ta bud’e froze chicken data gani ciki ta ciro takoma kitchen d’in. Soya masa tayi duka incase ko zeci zuwa rana. Flask ta nema ta juye ciki, tare da had’a masa coffee cikin flask sannan taje tayi arranging dining table masa. Daidai lokacin Anas yafito, k’amshin designer turarukan daya feshe kansa dashi tun daga sama har k’asa ne ya bugi hancin Fannah. Kai ta d’ago tana kallonsa. Sanye yake da ¾ wando fari da farar vest wanda ya bala’in masa kyau, ga wani sheqin da jik’ak’k’en gashinsa ke, kumburin fuskarsan ma ya ragu sosai, sede alamun ciwo da yankan dake ta bakinsa da gefen ido. Da sauri ta kawar da kanta kafin yace ta cika kallo dayawa. A hankali yake tafiyar har ya iso kan dining table d’in, zaman ma da k’yar yayi harda d’an k’ara “argh!” Tare da rik’e cikinsa. “Does it still hurts?” Ta tambayesa cike da damuwa. Kai ya girgiza mata amman ita tasan zafi yake masa. “I made you breakfast I hope you like it.” Yana kallonta tayi serving nasa kajin tare da juye masa coffeen cikin cup ta tura masa gabansa. “Zan jiraka a parlour, eat please.” Kallon abincin yayi sannan ya kalli Fannah. A hankali ta juya zata fice, hijabinta ya rik’o chak ta tsaya bata juya ba. “Lets eat together” yace da ita. “Sir naci abinci I’m full nagode.” “Please.” Ya fad’i wanda besan lokacin daya fad’a ba shi kansa, meke damunsa? Haka kawai yaji in ba ita bare iya cin abincin ba. ‘Please?’ ta nanata a zuciyar ta. Dagaske Mr. Fauzi ne yau yace mata please? Lallai! A nitse ta juyo, kujera opposite him ta zauna tana watsa da yatsunta. Plate ya jawo ya juye mata ragowar kazan duka. “Eat” yace da ita. Baki ta bud’e data d’ago kai taga uban kajin daya tara mata gabanta. “Sir ina zan kai wannan? Yayi yawa.” Hannu ta mik’a zata ja flask d’in a yayinda ya d’aga daga kan table d’in gabad’aya ba tare da yace komi ba. “Sir please ka rage yayi yawa.” Ignoring nata yayi “lets eat I’m hungry.” Nasa ya soma chi itako har yanzu bata tab’a plate d’in ba ina zata kai wanga kaji? “Miss Aleeyu eat.” Miyau ta had’iye a hankali ta d’au cinya d’aya ta soma ci. Zaman makokin ne ya isheta tayi gyaran murya sannan tace, “Sir do you want to talk about it?” Sanda ya nisanta sannan yace, “about?” Ba tare da ya kalle ta ba. “Abinda ya sameka.” Kai ya girgiza “No.” “Okay...” tace a hankali “but Sir next time ka kiyaye please koma mene neh.” “Okay” yace mata kamar d’an yaron da mamansa ke masa fad’a. Haka kawai yaji bayasan fad’awa Fannah gaskian al’amarin yasan definately zatayi blaming kanta zatace duk akanta fad’an ya tashi kuma hakan ne komai a sanadin ta ya faru sede bayasan tayi feeling guilty. “Sir?” ta kira sunansa. “Yes” ya amsa yana sipping coffeensa. “Mesa kace kar na kira Amal na sanar da ita I’ve found you?” “Saboda banasan susan inada gida anan.” Sam bata fahimce me yake nufi ba, so yake yace bawanda yasan yanada gida? “Ke kad’ai na fara kawo wa cikin nan, ko Shettima besan I have a paint house ba.” Meh Mr. Fauzi yake nufi kenan? Does this mean tanada wani matsayi a zuciyarsa da har ya b’oye wa kowa gidan sa hatta family’naa amman ita ya sanar da ita ya kuma barta tana shiga??? *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:53, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 4⃣3⃣ Bacci meh rai da lafiya Fannah tayi wanda ta jima ma batayi ba se chan bayan azahar ta tashi. A hankali ta bud’e idanunta jin kanta tayi kan pillow cike da mamaki ta duba harda bargon ma, toh waya shigo ya rufeta? Waya kunna mata AC? Ko kad’an bata kawo Mr. Fauzi arai ba saboda tasan halinsa, toh kode Yusuf ne? Toilet ta nufa ta wanke fuskarta tare da brushing sannan tafito ta ninke bargon tsab ta had’a da pillown sannan ta d’aga tafito dashi a hannunta floor na office nasu Yusuf ta nufa akan table nasa ta tsincesa bayan sun gaisa tace, “gashi nagode, shine akan ka tada ni narufe kaina kayi min wahala haka?” Cike da mamaki Yusuf ke kallon Fannah totally speechless. “Nikuma?” ya fad’a a k’arshe. “Ina zan samu bargo da pillow a office Fannah? Kode har yanzu baccin naki be wassake bane?” “Yusuf banasan wasa please amshi kayan ka, inkuma so kake kabarmin seka fito fili kace Fannah na baki.” Murmushi me sauti ya saki. “Fannah wallahi am serious ni banma san wai kina bacci ba kide zagaya ki tambaya waya sani ko Boss ne dakanshi nema ya rufe ki.” “Dariya kakeson bani komeh? Boss ya rufeni ina bacci? Impossible barinje in tambayi Ahmad da Kacallah.” “Zaki b’ata lokacin ki ne saboda Boss ya aikesu tun d’azu.” Yi tayi kamar bata jisa ba what if abinda Yusuf ke fad’i gaskia ne? ahaka har tashiga elevator ta hauro sama tana tsaye bakin k’ofar office na Anas amman takasa shiga inkuma ba nashi bane fah? Yace tacika shisshigi da k’yar de tasamu tayi knocking a hankali. Daidai Anas ya d’au bottle na beer nasa ze sha kenan knock yashigo. Haka kawai yau yaji yana san yad’an bugu saboda ya kwana biyu be sha ba tunda Fannah na bacci bare d’an sha abinsa kuma ba ma haka ba so yake yabar tunanin Fannah, ba abinda ya tsinana wa kansa yau, wai mesa ma yaje ya rufeta d’azu da take bacci? Tausayi ne ya fad’a a fili. I don’t love Fannah I just pity her yayi reminding kansa. “Who is it?” Ya tambaya. Chan murya k’asa k’asa a hankali tace, “Fannah ce.” Da sauri ya rufe bottle d’in tare da jawo drawer’n gefensa ya rufe. Turare ya feffesa cikin office d’in dan kashe warin giyan tare da kimtsawa sannan yace, “come in.” Tana shiga yaganta da pillow da bargon, kallonta yake har sanda ta k’ariso gaban table nasa. Shiru tayi tana nazarin taya zata fara masa maganan, shima shirun yayi tare da had’a hannayensa biyu k’ark’ashin hab’ansa yana kallonta kamar hoto. Can ta fara kamar haka; “Ermm Mr. Fauzi ban sani ba ko wannan naka ne, na tambaya su Yusuf duk sunce ba nasu bane.” Kallonta har yanzu yake da wani murmushin tsiya karara a fuskarsa. “Wato dan kin maidani dustbin shine zaki kawo min?” Kai ta d’ago tana kallonsa “No Sir ba abin da nake nufi ba kenan-” katseta yayi “Shine mana, kin tambayi saurayinki Yusuf yace ba nashi bane shine kikace bari ki kawo wa dustbin shikam ze karb’a koba haka ba?” “No Sir thats not what I mean, in ajiye maka a ina?” “Ba nawa bane” ya bata takaicaccen amsa. Kanta ne ya d’aure. Kamar ya ba nasa ba? Toh na waye? Ita se yanzu ma ta tuna ranan da Mr. Fauzi ya rufeta a d’akinsa ai taga bargon nan akan gadonsa, to mesa zece ba nasa bane? “Sir but ranan naga bargon nan a d’akinka.” “Aww mak’aryaci kikeson ki kira ni dashi kenan, ince miki ba nawa bane kice nawa ne” “No Sir ba abinda nake nufi ba kenan.” “Inma tunani kike wai da kike bacci ni naje na rufe ki toh you are mistaking dan ni ko shiga office naki banyi ba.” “I’m sorry” tace cike da kunya ita de tasan ranan tabbas taga wannan bargo a d’akin Mr. Fauzi kuma gashi yace ba nashi bane. “Jeki ajiye kidawo am waiting for you.” Bayan minti d’aya Fannah ta dawo “yes Sir.” So yake ya ce mata suje suci abinci amman girman kai ya hanasa. Seya bud’e baki ze fad’a se yayi shiru. Ganin baida niyyan magana Fannah tace, “Sir you called me.” “Ina sane ai” yabata amsa. “Ko ban tambaya bama nasan kinajin yunwa lets go and eat.” ya fad’a in an I dont care tune. Qarya tayi niyyan masa tace tana azumi seta tuna yasan batada tsarki. “Sir I’m not hungry thanks.” “Toh ni inaji lets go” zata sake magana yace, “banasan musu” bayan sa ta nufa bayan ya rufo k’ofar office nasa Fannah ta juya zata nufa public elevator, hijabinta ya rik’o. A tsorace ta juyo tana kallon had’add’un yatunsa daya k’ayata su da zobunan azurfa masu tsada rik’e da hijabinta sannan back to fuskarsa. Beso suka had’a ido ba “mu shiga nawa” yace mata. Kai ta giad’a masa a sanyaye tabi bayansa suka shiga private elevator’nsa ba wanda yace ko uffan ahaka har suka sauk’a driver yayi driving nasu zuwa wani hotel na daban ma yau. Abinci me rai da lafiya Anas ya mata ordering. “Eat” yace mata alokacin daya d’aga spoon nasa, ba musu ba gardama itama ta d’au spoon suka soma ci. Ko da yagama cin nasa zaman jirarta yayi data gama ya tambayeta, “a k’ara miki?” Kai ta kad’a masa bayan ya biya suka koma office d’an errands kad’an Fannah tayi wa Mr. Fauzi, lokacin tashinsu nayi ta wuce gidah. Shima Anas yana gama abinda yakeyi ya kama hanyan gida, tuk’i yake hankalinsa kwance ya d’ibo bottle na giyansa biyu yau a paint house nasa ze kwana, unguwar shiru yake ba mutane sosai yana cikin tuk’i yaga mota ya fito from nowhere yayi blocking nasa, ikon Allah ya tsaya gani reverse ya gwadayi a take yaga bayan san ma anyi blocking. Toh su waye ne? Kafin yanemi amsa wa tambayan daya ma kansa yaga maza uku sun fito daga motar gaban nasa da angansu anga ‘yan maye ‘yan bayan gari. Murmushi kad’an ya saki dan in ‘yan su uku ne acikin minti biyar ze gama dasu. Kafin ya yi yunk’urin yin wani abu yaji ana knocking jikin window’nsa. Window’n yayi wining “munada problem neh?” Ya tambaye gayen. “Dade ka fito tukuna.” cewar gayen. Ba gardama ya fito ya tsaya nanne yaga duka duka mazan guda biyar ne. “Will you guys let me pass or senayi muku abinda bakuwa so?” Familiar murya ya jiyo daga behind nasa yana cewa; “Kokuma mu mu maka abinda baka so ba Mr. Fauzi” yana kai dubansa gun da ya jiyo muryan idanunsa suka sauk’a kan Farouq yawani pake kan driver’s sit cike da isa ya taso tare da takowa gunsu Anas. “You’ve had your time the other day now is mine.” Wani erin dariyan rainin hankali Anas ya saki harda tafi “you are such a genius Farouq. Wai ka d’au dakai da wannan mashirmatan daka taran zaku iya min wani abu ne?” Dariyan bosawa Farouq ya saki “Mr. Fauzi kenan kasani sarkin yawa yafi sarkin k’arfi. Apologise to me, tell me sorry akan abinda kamin jiya and I will let you a save passage.” “Ni in ce maka sorry?” Yayi murmushi “never!” “ATTACK!!!” Farouq ya fad’i nan maza biyar d’in suka soma nufuwa wajen Anas. Sleeves nasa yayi rolling tare da ciro Rolex agogonsa kafin ace me suka b’arke cikin mumunar fad’an BIYAR akan D’AYA. Farouq na tsaye a gefe yana kallon yadda Anas yake destroying masa mutane, duk se kamar yafi k’arfinsu dukda suma suna k’ok’ari dan har sun fasa masa baki amman yafi cin uwarsu. Tsawa Farouq ya daka musu “wai zakuce shi kad’ai yafi ku duka k’arfi ne?” Ai se kamar maganar Farouq k’arfi ya k’ara musu. Sunayi Anas yanayi har suka samu sukaci galaba akansa hanci, baki ba wanda basu fasa masa ba. Hannayensa suka kama ta kowani gefe a lokacinda Farouq ya taso daga inda yake. “Ohhh look at you Mr. Fauzi abin tausayi, ina k’arfin naka yaje? Ina polisawan naka? Kud’in ka ya ceto ka mana.” Fuskar Mr. Fauzi dayake yoyon jini Farouq ya d’ago “tell me meh had’inka da mata ta Fannah?” Murmushi Anas yayi dukda azaban dayake ji. “Kaikuma tell me meh had’inka da alak’a na da ita? Mind your damn business.” “Bakinka be ruhu ba kenan har yanzu. Rik’e min shi dakyau” yace da mazan nasa. Gagam suka sake damk’e Mr. Fauzi punch me rai da lafiya Farouq ya kai masa wanda seda idanun Anas suka juya. “Nace meh alak’arka da matata?” “Fannah is not your wife” ya fad’a a wahalince. “Take note” “Har yanzu baka bugu ba.” Naushi yakai ma Anas a ciki wanda sakamakon hakan ya saki k’ara sosai dan azaba. “For the last time me had’inka da Fannah?” “Kanason kaji me had’ina da Fannah? *FANNAH IS MY GIRL, I LOVE HER.*” Cike da b’acin rai Farouq ya cukumo kolar rigan Anas “me kace? Sake nanata abinda ka fad’a inji” “I LOVE FANNAH, KUMA NI ZAN AURETA BA KAI BA, FANNAH TAWA CE!!!” “You really want to die.” Naushi lafiyayyu guda uku ya kai wa Anas aciki biyu kuma a fuska. Kaca-kaca suka ma Anas, duk wanda ya kallesa bare so sake sa idanunsa kansa ba duk jikinsa jini. “Me alak’ar ka da Fannah? Kace min baka son ta kuma baka santa ba.” Da k’yar yake maganan “NEVER!! I LOVE FANNAH, ko kasheni zakayi bare canza komai ba.” A fusace Farouq yace, “Baaba” na gefen daman Anas “je cikin trunk na motan can kaciro min sandan chan nakega inba dukan mutuwa na masa ba bare shiga hankalinsa ba. Zakace baka son Fannah ko yaya?” Shiru Anas yamasa bece komai ba se nishin wahalan dayake yi abin tausayi. “Farouq ga ‘yan patrol zuwa fa!” Baaba yayi exclaiming da ihun gaske ai kamar kyaftawan ido su Farouq suka lodu a mota suka bar wajen a 360. Anas na kwance helplessly a k’asa. Bayan motan patrol d’in ya k’ariso polisawan suka diddiro ganin mutum a k’asa, plate number’n motar Anas d’ayan ya karanta yaga “Mr. Fauzi.” “Guys Mr. Fauzi ne!” da gudu sukayi kansa suka d’ago sa zuwa motar sa tare da miqar dashi a back seat. “Abba lets go, mu kaisa asibiti push the start button.” d’ayan officer’n ya fad’i. A wahalince Anas yace, “no karku kaini asibiti just drive me home, to my paint house.” “Sir but you are badly injured.” “I know, ku kaini paint house d’ina kawai.” “Okay sir ina ne paint house d’in?” Nan Anas ya musu kwatance murya yana d’aukewa. “Sir su wa suka maka haka?” Har ya bud’e baki ze kira sunan Farouq seya tuna in ya fad’a musu definately zasu kama Farouq su rufe sa kuma, in hakan ya faru kuwa Fannah barata ji dad’i ba. “Nima bansan suba” yama officers d’in k’arya “ ‘yan iskan unguwa ne kawai.” Daidai gaban paint house nasa suka iso. “You can go now zan k’arasa da kaina nagode.” Cewar Anas idanunsa suna kafewa. “Sir amman kace barakaje asibiti ba? Wannan mutane sunji maka ciwo fah.” “Don’t worry I can take care of myself.” Bottles na giyansa guda biyu yaciro da k’yar yake iya tafiya dan kalan dukan dayasha wajen Farouq da mutanensa, ahaka har ya samu ya isa ciki ko k’ofan ma yakasa locking. Bayi ya nufa da rarrafe da taimakon sink ya mik’e ya kalli fuskarsa a madubi. Sam beso sake kalla ba dan irin ciwon da suka ji masa. Ruwa ya gwada wanke fuskar nasa dashi. Aiko ruwan na tab’a fuskar ya saki k’ara dan azaba daga k’arshe hak’ura yayi yakoma d’aki tare da rage kayan jikinsa yabar short nicker kawai. Kwalba d’aya ya kwankwad’e tas dan samun bacci, yana shanye wa kuwa bugeggen bacci ya d’ibesa ko sallan maghrib beyi ba bale na isha. Wayoyinsa dake cikin mota kuwa se kiransa su Ummie suke ba iyaka amman bai d’aukawa hankalin kowa ya tashi, ko da sukaje office nasa suka tambaya kuwa, kowa ya shaida Mr. Fauzi yabar building d’in lafiya. ***** _Washegari..._ 8:10AM yama Fannah a office sede tata knocking a bakin k’ofar office nasa amman shiru chan ta gwada bud’ewa taji a rufe alaman Mr. Fauzi bezo bama kenan! To meya rik’esa? Shida ko lattin minti d’aya baya yi. Meya faru? Mesa bezo ba? Ko baida lafiya ne? Minti 15 ta k’ara tana jiransa amman ba alamansa. Gashi yanada board meeting by 10:30AM. Ganin ba mahalicci se Allah kawai ta sauk’a k’asa ta samu Kacallah tare da tambayansa ko sunyi waya da Mr. Fauzi. “A’a wallahi nima Fannah na kirasa ta duka layinsa baya d’agawa tun jiya na rasa dalili.” Kawai setaji gabanta na fad’i. “Toh nagode” tace masa. Wayarta taciro ta kirasa har ya tsinke be d’aga ba. Tashin hankali. To ina yashiga? Amal ta kira ta tambayeta ko Anas na gida cike da tashin hankali Amal tace mata itama tun jiya suke neman Anas bedawo gida ba. Napep ta tsara bata tsaya ko inaba se paint house na Anas motarsa tagani fake gaban gidan wani hamdala tasaki har ta ciro wayarta zata kira Amal ta sanar da ita se kuma ta fasa, bari de ta tabbata ko yana ciki tukuna. Door bell ta danna sau uku amman ba response. Tana gwada murd’a hannun taga k’ofar abud’e ba sak’e sak’en da bezo mata ba toh kode barayi ne suka shigo masa? Subhanallah amman ai kuma ga motarsa. Ciki tashiga ta lek’a kitchen ba alaman ko motsin mutum “Mr. Fauzi!” ta kira sunansa shiru d’ayan d’akin ta bud’e taga nan ma bayanan toilet dinma haka, guest toilet ma ta duba bata gansa ba. Daga k’arshe d’ayan d’akin ta bud’e a hankali kwalban giya ta soma cin karo dashi, se fad’i gabanta yake ta d’aga tare da k’arisawa cikin d’akin tana taku a hankali cike da tsoro. “Mr. Fauzi!” Ta kira sunan sa alokacin data gansa kwance kan gado yayi ruf da ciki se bacci yake yi ba ko riga jikinsa se bedsheet daya ja zuwa tsakiyar cikinsa. A nitse ta k’arisa gefen gadon tare da ajiye kwalban kan side drawer. “Mr. Fauzi!” Ta sake kiran sunansa shiru be amsa ba. Toh kode mutuwa yayi ne? Sede kuma tajisa yana numfashi. Jijjik’asa ta hau yi har se lokacin daya soma motsawa. “Waye ne?” Ya tambaya cikin bacci. “Sir Fannah ce, Fannah Aleeyu.” “Fannah? Me kikeyi anan? Ban rufe k’ofan bane?” “Eh sir baka rufe ba, you need to get up kanada board meeting by 10:30AM.” Cikin bacci yace, “barinje ba kiyi cancelling, tell them barin samu zuwa ba.” “Sir but why? Kayi hak’uri ka tashi please.” Bece da ita komai ba ya cigaba da baccinsa. Pillow’n daya rufe fuskar sa dashi ta d’aga. Ido ta zaro tana salati alokacin da taga irin ta’addancin da aka ma Anas a fuska. Meya samesa? Waya masa duka haka? “Subhanallahi Mr. Fauzi meya sameka? Omg!” ta tambaya a kid’ime a lokacin da ta tsuguna gabansa. Da k’yar ya iya bud’a baki yace, “ki rufe min fuska banasan hasken nan.” Ignoring nasa tayi “Mr. Fauzi waya maka haka da fuska? Fad’a kayi da wani neh? Meya sameka?” “Bansani ba nima just leave me get out.” Haka kawai yaji baya san Fannah tagansa a bad condition irin na yau, bayasan yasa ta cikin damuwa bayasan taji tausayinsa. “No Mr. Fauzi I’m not leaving you like this.” Hannu tasa ta dafe goshinta bata ma san ta ina zata fara ba. Hawaye kawai taji yana gangaro mata kan kumatu dan uban tausayi irin nata. Hannu ta aza ta tab’a gefen idansa daya kumburo dan bugun daya sha. K’ara ya saki wanda yasa ta mayar da hannunta baya da wuri. “Sorry” tace cikin kuka. Idanunsa na sauk’a kanta yaga tana hawaye abinda baya so kenan. “Miss Aleeyu leave please, goo.” “I can’t leave you like this, Mr. Fauzi asibiti yakamata muje su duba ka.” “Barinje ba” yabata takaicaccen amsa idanunsa a rufe. “Please” ta rok’esa tana hawaye ganin yadda aka masa destroying kyakkyawar fuskarsa da a yanzu mutum bare so ya kalla sau biyu ba. *© miemiebee* b[truncated by WhatsApp] [12:53, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 4⃣5⃣ *THANK YOU SO MUCH DA ADDU’O’INKU MASU SO DA K’AUNA TA, ALHAMDULILLAH NAJI SAUK’I SOSAI* Shiru tayi bata ce komi ba as tana nazarin abu a ranta. “Say it out” yace yana kallonta. Mamaki ne yacika ta how comes ya gane ta nada magana a ranta. “Errm babu” tayi k’arya. “Akwai say it.” “I was thinking ko za’a zubar da abubuwan da suke cikin fridge d’in kar in-” katse ta yayi “jeki d’iba ki zubar, kiyi flushing duka.” Dad’i sosai taji nan take ta mik’e. “After kin gama cin abincin ki amma.” “Sir na k’oshi thank you” bata tsaya jiran me zece ba ta nufa fridge d’in tafito da duka kwalabe guda 15 d’in. “Sir akwai wani bayan wad’annan?” kai ya gyad’a mata. “Are you sure Sir?” Kai ya girgiza “akwai kwali d’aya k’ark’ashin gado na a d’aki.” “Thank you Sir.” Uku-uku ta riga d’iba tana kaiwa toilet tana zubarwa har tagama duka kwalaben kuwa tayi disposing nasu. Bayan ta gama ta d’au first aid box daga toilet tafito dashi zuwa dining space inda ta tsinci Anas zaune yayi zurfi cikin tunani. “Sir?” Ta kirawosa tare da dawo dashi daga duniyar tunanin daya wula. Kallonta kawai yayi ba tare da yace komi ba. “I think ciwon fuskan kan zefi healing da wuri in aka rufe” ta fad’i tana ciro wasu transparent bandages guda biyu. B’antare d’aya tayi. “May I?” Ta tambayesa kai ya giad’a mata nan ta manna masa na gefen bakin nasa a hankali sannan na kusa da idansan shima a hankali. “Get well soon” tace dashi a lokacin data rufe first aid box d’in ta mayar toilet, fitowarta ta nufi bakin k’ofa. “Miss Aleeyu” ya kira sunanta chak ta tsaya tare da kewayo wa. “Yes Sir.” “Ina zakije?” “I’m going home, jikin naka da sauk’i ba?” Alokaci d’aya kuma se yaji bayasan ta tafi, shi yake korarta d’azu amman yanzu kuma so yake ya cigaba da kasancewa *_TARE DA_* ita, bayasan ta tafi wanda shi kansa besan dalili ba. “Must you go?” Ya tambayeta. A hankali tace, “Sir I have to, bareyi in cigaba da zama anan ba.” “Okay” yace blankly. Bata ce dashi komai ba ta fice. So yake ya tsayar da ita yace mata ta zauna dashi baya san ta tafi amman bayasan ta raina sa bayasan ta d’auka da wata manufa, ta zata ko santa yake. Isar Fannah gida ke da wuya ta tarar da Farouq tsaye bakin k’ofa da alama ita yake jira. Bugun zuciyarta taji ya k’aru in akwai d’an Adam data tsana a doron k’asa toh Ya Farouq ne. Bayan ta sallami meh napep d’in ta sunkuyar da kanta tayi kamar bata gansa ba se tafiyarta take a yayinda idanunsa suke biye da ita. Takai da shiga cikin gidansu kenan kawai Farouq ya jawo ta da k’arfin gaske, kafin tayi yunk’urin yin wani abu ya matseta jikinsa gagam shi a dole yana hugging nata. “Ya Farouq me haka? Ka sakeni” se k’ok’arin k’watan kanta take amman ta kasa. Batasan lokacin data fara kuka ba. Se bugin k’irjinsa take amman kamar super glue yak’i sakinta. “Fannah mesa bara ki soni ba? Mesa Fannah? Ke bakisan ina sonki bane? Akan ki kowa ze iya mutuwa, mesa se wancan me idan turawan zaki so? Me yake dashi da banida? Tell me mesa bakiya sona?” ya k’are maganar yana wani erin zakin nishi kamar ze cinye ta tare da shunshuna hijabinta sekace ze cire. “Ya Farouq ka sake ni dan Allah zan fad’a maka dalili.” Chak ya sake ta, “fad’a min my Fannah.” “Ya Farouq bana sanka yaci ace ka hak’ura inhar kanaso na kamar yadda kake fad’i abinda nakeso ya kamata kamin, ka hak’ura you and I are not meant to be please ka fita daga hark-” bata k’are maganar ba ya tsinke ta da wani erin wawan marin da take ga ba’a tab’a mata ba erin sa ba, gefen bakinta ne ya fashe take yana zubda jini, harwani kurma-kurma tazama for the mean time. Kukanta ne ya tsananta a yayinda taga jini na fita daga gefen bakinta. “Bakiya so na? Bakiya sona se wancan d’an iskan?” Hannunta ya rik’o cike da mugunta. Cikin kuka da azaba tace, “Ya Farouq dan Allah ka sake min hannu da zafi...” “Toh wallahi baki isa ba, inada tabbacin kinga halin da Mr. Fauzi yake ciki wallahi in be fita ya bar harkarki ba kinji na rantse har kashe sa senayi kamar yadda nasa aka masa duka.” Ita bata damu ma da kanta ba yanzu, Mr. Fauzi ne damuwanta. “Ya Farouq yanzu kai kama Mr. Fauzi duka haka sekace kashe sa zakayi, me ya maka?” Ta tambayesa tana hawaye. “Yace min yana sanki abinda yamin kenan, nikuma muddin ina raye ba mahaluk’in daya isa yace yana sanki, ke tawa ce Fannah, you are mine! Inhar kinasan Mr. Fauzi ya rayu toh wallahi kifita daga harkansa kije kiyi ending up duk wani abinda ke tsakanin ku ni na fad’a miki if not next time gawansa zaki tsinta.” Mr. Fauzi yace yana sona? Abinda ta nanata kenan a ranta. Ya fad’i hakan ne dan kareni daga Ya Farouq badan yana sona tsakani da Allah, banida standards da Mr. Fauzi ze gani har yace yana so na. “Ya Farouq dan Allah badan ni ba, whatever that is going on between us karka sa Mr. Fauzi aciki ba abinda ya maka dan Allah.” “Rai da lafiyan Mr. Fauzi lies in your hands, kifita daga harkansa tell me you love me zaki aureni as soon as possible and ba abinda ze sake samin Mr. Fauzi kinji my wifey?” “In nayi haka zaka fita daga harkansa baraka sake tab’a lafiyar sa ba?” Ta tambayesa tana hawaye ba makawa. “Eh my wifey kika min haka ba abinda ze sake tab’a lafiyar Mr. Fauzi.” “Okay Ya Farouq I will do it, na yarda zan aure ka amman karka sake tab’a Mr. Fauzi dan Allah.” “Bar kuka tawan, tell me you love me” ya fad’i yana k’ok’arin rik’e hannunta. Hannun nata ta rik’e gam a jikinta hanasa yin bainda yayi niyyan yi. Cikin kuka cike da tashin hankali tace, “Ya Farouq I love you zan aure ka, please kar ka sake tab’a Mr. Fauzi.” “Good girl, sesa nake sonki akwai sanin yakamata. Bar kuka toh kinji banasan ganin wannan hawayen” jinin dake mak’ale a kusa da bakinta yasa hannu ze goge a yayinda ta ja da baya cike da tsoro. “Jeki huta sena dawo gobe se ayi maganan auren namu ko?” Shiru tayi bata amsa saba. “Koh?” Ya sake tambaya. “Eh” tace masa. “Toh ni zan wuce, I love you” jira yake ta amsa masa da ‘I love you too’ yaji tayi shiru. “Wifey baraki cemin I love you too bane ko bakijini bane?” Kamar wacce baratayi magana ba can tace, “ban jika ba.” “Yanzu kin jini ai ko? So answer me.” Shiru tayi bata ce komi ba. Hannunta ya cafko cike da mugunta. “Tell me abinda nakeson ji.” A wahalince tace, “Ya Farouq I love you dan Allah ka sake min hannu da zafi.” “Say it again.” Yayi demanding. Tana hawaye tace, “I love you ka sakeni please.” Wulli da ita yayi sannan ya fice. Har k’asa ta sauk’a tana kukan takaici na kusan minti ishirin, sanda tayi me isarta sannan ta mik’e tashiga ciki bakowa tsakar gidan daga d’akin Baba ta jiyo sautin hirar su. D’akinsu dasu Afrah ta nufa ta baje kan gado “mesa Mr. Fauzi? Mesa baka fad’a min Ya Farouq bane ya sa aka maka duka? Mesa kak’i fad’amin?” Wayarta ta zaro daga jakarta ta kira layinsa sede har ta tsinke be d’aga ba. ***** Da tunanin Fannah arai Anas yayi bacci yak’i komawa gida saboda bayasan acika sa da surutu. Su Ummie de da tashin hankali na kisa da yayi musu, dan ko damuwa Anas ya ciro wayoyinsa daga mota beyi ba yini yayi yana tunanin Fannah. _Washegary..._ K’arfe 8:00AM on the dot yama Anas a office, sosai kowa yaji dad’in dawowarsa. Fannah kuwa 8:03AM ta hallaro. Yasan fuskan nan, yasan mood da Fannah ke ciki yau dole abu na damunta. “Good morning Sir, how are you feeling?” ta gaishesa a hankali kanta a sunkuye. Beko damu da gaisuwar nata ba damuwansa ya ji abinda ke damunta. “Miss Aleeyu” ya kira sunan ta a hankali. “What’s wrong?” Ya tambayeta cike da damuwa. Kanta still a sunkuye tace, “babu” a hankali. “Look at me Miss Aleeyu.” bata ko motsa ba. “Look at me, will you?” ya sake fad’a. Idanunta dasuka cike da hawaye ta d’ago tana kallonsa, sun kumbura iya kumbura dan yadda ta kwana tana kuka, ba kalan hak’urin da su Mani basu bata ba ammsn tak’i dena kukan. “Mr. Fauzi I’m so sorry, I’m terribly sorry mesa baka fad’a min ba? Mesa ka b’oye min abinda Ya Farouq ya maka? Mes-” kukan ne yafi k’arfin ta takasa k’arisa maganan. Baro kujeransa yayi cike da tashin hankali da tausayi ya matso ya tsaya kusa da ita tare da ciro hanky daga aljihunsa yana share mata hawaye, the more yana share mata the more kukan nata yana tsananta. Se a yanzu yaga alaman gurji a fuskarta. Kukan take har yanzu bece mata sorry ba be kuma hana ta ba. Yasani kukan ne kawai ze sata feeling better. Sanda tayi me isarta sannan tayi shiru da hijabinta ya jata zuwa kan kujera suka zauna. “Me ya sameki Miss Aleeyu? Waya ji maki wannan ciwo?” Kai ta kad’a masa “babu kawai naji ciwo ne” ta masa k’arya. “Zan koma office d’ina, I’m sorry ban samu na had’a maka schedule naka ba, excuse me” “Miss Aleeyu look at me.” A hankali ta d’ago jajayen idanunta da suka kumburo ta sauk’esu kan Anas. “Meya sameki? Waya ji maki wannan ciwo? Forouq ne?” Kai ta kad’a masa dan bata son abinda ze sake had’a sa da Ya Farouq batasan Ya Farouq ya sake sa a masa duka kamar yadda yasa aka masa shekaran jiya. “You are lying” yace. “Mr. Fauzi it doesn’t matter-” katse ta yayi; “Yes it matters” ya fad’a a tsawace. “I can take duk abinda Farouq zemin amman inya tab’aki I can’t let that go. Banasan hankalinki ya tashi shiyasa ban fad’a miki ba, banasan kishiga damuwa. Miss Aleeyu I don’t know why amman banasan ganinki cikin danuwa, tell me Farouq ne ya miki wannan abu?” A hankali kalamunsa suka sauk’a cikin kunnen Fannah. “Eh shine.” Take yanayin nishinsa ya canza wanda ta gano hakan. “Marinki yayi?” rai a b’ace yayi tambayar. “Sir is okay-” “Its not” ya katse ta a fusace. “Marinki yayi?” Shiru tayi bata amsa saba ita tsoronta d’aya ne kar Mr. Fauzi yace zeje ya sami Ya Farouq su sake b’arkewa da wani fad’an. “Miss Aleeyu I’m talking to you.” Kai ta giad’a masa a hankali. “He has crossed the line this time around” mik’ewa yayi a fusace a yayinda ta rik’e suit nasa ta k’asa “Sir please let him be, hakan shine kwanciyar hankalin mu.” “Miss Aleeyu me kike nufi?” Ya tambayeta cike da rashin fahimta dakuma tausayi. “Mr. Fauzi Ya Farouq promised me bare sake maka wani abu ba in ka fita daga harkanshi so please karka je ka samesa akan wannan d’an ciwon daya ji min.” “Me kike nufi Miss Aleeyu? You are hiding something, tell me. Haka kawai Farouq bare ce ya hak’ura ba. Tell me meh kikayi promising nasa in return?” “Babu” ta fad’i a takaice. “As your Boss tell me, will you?” Ya fad’i a d’an tsawace. “Mr. Fauzi Ya Farouq yace only if zan aure sa bare sake tab’a lafiyar ka ba, I agreed to it banason saboda ni wani abu ya sake samunka please ka fita daga harkansa kayi hak’uri kuma kan abinda ya maka in ba haka ba Ya Farouq might kill you.” Ta fad’i hawaye na ciko mata a ido. “Miss Aleeyu mesa zaki auri Farouq bayan bakiya sansa?” “To protect you Mr. Fauzi, Ya Farouq mutumin banza ne yadda yace ze iya yin kisan kai nasan sa tunba yau ba, tsab ze iya kashe rai saboda yadda yakeson ya aure ni so please stay out of his business.” “No Miss Aleeyu I can protect myself, ba sekinyi protecting d’ina ba am not afraid of Farouq in a yau kikeson dena ganinsa a yau d’in za’a rufesa.” “Mr. Fauzi koda an rufe sa definately one day ze fito, fitowarsa kuwa shine asalin babban tashin hankali a garemu duka dan bare barka ba seyaga k’arshen ka abinda baran iya juran gani ba kenan. Kawai dan Allah ignore him please.” “Miss Aleeyu you don’t have to marry him for my sake ba abinda Farouq ze iya min, please karki auresa.” “Mr. Fauzi banida wani option, aurensa shine zaman lafiyan mu all, ni kawai dan Allah karka sake shiga harkansa please.” Hawayen dake gangaro mata tasa hannu ta share tare da mik’ewa tabar office d’in tana fita shima yabi bayanta hannunta ya rik’o gam ta yadda barata iya k’wata ba. Kuka take sosai “Mr. Fauzi ka sake min hannu.” “Shut up!” ya daka mata tsawa, “that fool will pay today” zuciyarsa tafasa yake ze iya d’aukan duk abinda Farouq ze masa amman banda abinda yayi wa Fannah, how dare he slap her har ya ji mata ciwo?? *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:53, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 4⃣6⃣ Wajen elevator’nsa ya jata bayan sun shiga tace, “Mr. Fauzi where are you taking me to?” Be amsata ba illa wayansa da ya ciro daga aljihunsa yayi waya wanda ga dukkan alamu da polisawa ne. Bayan ya gama Fannah ta maraice “Mr. Fauzi not again please, kayi hak’uri dan Allah.” Beko saurare ta ba. Bayan da elevator’n ya bud’u yaja hannunta daidai gaban motarsa ya tsaya tare da bud’e k’ofar gaba wa Fannah. “Enter” yace ba tare da ya kalleta ba. Dakewa tayi “barin shiga ba Sir, kabari mana dan Allah duk abinda ka masa yanzu nasan Ya Farouq he will fight back, fad’an ya cigaba kenan kuma.” “Get in the damn car!!” ya fad’a a tsawace. Ta tsorta iya tsoro amman kuma tak’i shiga. “Miss Aleeyu I said get in, karki bari raina ya b’aci in d’aga ki in saki ciki da kaina.” “Sir promise me ba wajen Ya Farouq zamuje ba.” Kai ya giad’a. “Promise?” Ta tambayesa. “Yes” ya bata amsa nan ne tashiga bayan ya rufo k’ofar ya zaga ta driver’s side yashiga shima. This is the first time yake driving nasu bibbiyu. Ganin hanyan gidansu yake nufa tace, “Sir you promised kace ba wajen Ya Farouq zamuje ba dan Allah ka juya.” Banza da ita yaui sanda suka isa gidan yayi parking tare da fitowa a fusace ya zaga ya fito da Fannah hannunta rik’e cikin nasa tayi tayi ta k’wace amman ta kasa. Ai kaman an turo Farouq se gashi ya yanko corner’n gidan hankalinsa kwance yana tafiya idanunsa suna sauk’a kan Anas yaga yadda yawani rik’e hannun Fannah. Ita kuwa ganin Farouq ta cigaba da k’ok’arin k’watan hannunta daga na Anas amman ta kasa. “Stop it” yayi warning nata. “Sir please ka sakeni kafin ya k’ariso.” Nan da nan Farouq ya iso gabansu se nishi yake kaman zaki dan wani bak’in kishin daya rufesa. Hannun nasu ya sake kalla sannan ya kalli Fannah, kanta ta sunkuyar tare da lab’ewa bayan Anas a hankali tace, “Ya Farouq I can explain this dan Allah kayi hak’uri, Mr. Fauzi please ka sakemin hannu.” “Bakaji me tace bane?” Ka sake mata hannu. “Banji ba” Anas yace kamar kyaftawan ido ya sake hannun Fannah tare da cikumo kolar rigan Farouq punches guda uku lafiyayyu yakai masa har k’asa Farouq ya sauka se zuban jini fuskarsa yake. Binsa k’asan Anas yayi tare da tsugunawa a kansa da k’afafunsa side-by-side na Farouq. Nan ma be bar kai masa bugin ba. Fannah dake basa hak’uri har bakinta yayi dogo “Mr. Fauzi please ya isa.” Se huci yake yana dukansa ba makawa. Hannun Mr. Fauzi ta gwada rik’ewa ya k’wata abinsa da zafi sauran kad’an ta fad’i k’asa. Ganin an kusan sumar da Farouq Fannah ta ruga a guje tare da hugging Anas ta baya cije da tashin hankali, abinda kad’ai yazo mata kai kenan duk da tasan yin hakan haramun ne, in bahakan tayi ba tana ganin Anas ze iya kashe Farouq da yadda yake ta kai masa bugi. Hannu ya d’aga ze sake kaiwa Farouq punch yaji jikin Fannah a nasa, wani irin electrification ya jiyo a jikinsa tun daga tsakiyar kansa har k’afa, wanda be tab’a ji ba tunda yasan kansa. Hawaye take sosai wanda har kad’an daga ciki ya tab’a rigarsa “Mr. Fauzi please ya isa dan Allah kayi hak’uri in ka cigaba zaka kashe sa ya isa dan Allah, please...” Se kuka. Ganin jikinsa ya mutu ta matsa baya tana share hawayenta mik’ewa yayi ya nufa wajenta “is okay kukan ya isa kinji?” Numfashi take ja dan yadda tasha kuka “please ya isa Sir karka sake tab’a masa.” Kai ya gyad’a mata “stop crying.” Itama kan ta giad’a masa. Da k’yar Farouq ya mik’e se jiri ke k’ok’arin d’ibansa, fuskar nan nasa ya ninka abinda yasa a kayi wa Anas, kayan sa duk ya b’aci da jini, da k’yar yake maganar a wahale. “Wallahi Mr. Fauzi you won’t get away with this, Fannah tawa ce! Fannah mata tace! Ni zan auri Fannah!” “No Farouq you are wrong *FANNAH TAWA CE! FANNAH MATA TACE! NI ZAN AURI FANNAH* and not you.” Shi kansa besan sanda yafad’i wannan kalamu ba. Fannah kam mutuwan tsaye tayi. Daidai lokacin motan polisawan suka iso guda biyu. Handcuff aka sawa Farouq a hannu “wallahi Mr. Fauzi kasani you won’t get away with this, duk ranan da na fito se na k’wato Fannah daga gareka, sena kashe ka in ban kashe ka ba sena kashe ta dan in barin samu Fannah ba, bawanda ze same ta.” Kansa aka tusa cikin motar. Daidai lokacin Ya Khaleel ya hallaro shima, ganin d’ansa cikin motan polisawa ya falfala da gudu izuwa wajen. “Officer ina zaku kaimin d’a dan Allah ku sako shi kuyi hak’uri. Farouq me kayi?” Nan ya juyo wajen Anas da Fannah. “Mr. Fauzi dan Allah kayi hak’uri kasa su sake min d’a wayyo Allah! Kayi hak’uri dan Allah bare sake ba.” “Ka sake had’a ni da Allah believe me kaima zaka bisa cell d’in. Take him away” yace da polisawan. “Fannah dan Allah karki bari atafi miki da miji ki rok’i Mr. Fauzi please.” Hawaye sosai Fannah take dan tausayi irin nata setaji duk she is ready to forgive them abubuwan da suka mata. “Mr. Fauzi dan Allah kayi hak’uri.” “NO” yace mata a tsawace “take him away, NOW!” A 360 suka bar wajen da Farouq. Kuka Ya Khaleel yake “Allah ze sak’a min wallahi, d’a na be maka komai ba kasa aka tafi dashi simply because kaga baida gata in shaa Allahu zan tara kud’i inyi bailing nasa, kekuma Fannah kisani Farouq shine mijinki ba wannan dayake miki wasa da hankali ba.” Yana kaiwa nan ya fice. Kuka me sautin gaske Fannah ta fashe da, “Mr. Fauzi why? Dan Allah ka dawo dashi I beg you please, banasan ka mutu, banasan wani abu ya tab’a ka. Ni nace zan aure sa ka sa a sakar dashi, ka sakar min miji.” “*Nine mijinki Miss Aleeyu* and that stays that.” Cikin kuka tace, “what are you saying Mr. Fauzi kana cikin right mind naka kuwa taya zakace kaine mijina? Ko baka san ba’a wasa da kalman aure bane? Ni ka sa su sake Farouq kawai dan Allah.” “Yes Miss Aleeyu nasan me nake fad’a ni zan aureki ba Farouq ba, you are going to be my wife” hannunta yaja tare da zaunar da ita cikin motar. Shima ya zaga ya zauna. Hawaye take sosai “Miss Aleeyu for goodness sake kukan ya isa. I’m going to marry you so as to protect you from Farouq atleast duk rashin kunyarsa inyaga ke matar aure ce ze saurara miki koda Babansa yayi bailing nasa, marry me Miss Aleeyu.” Kai take girgizawa continiously No! No! No! This can’t be happening bareyi in auri Boss d’ina koba dan haka bama bareyi in barsa ya aureni ba, *BANIDA BUDURCI, BANIDA MARTABA* duk ranan da Mr. Fauzi ya gano hakan ze tsaneni fiye da yadda ya tsani mutuwar sa, I can’t marry him saboda barin iya fad’a masa sirri na ba kamar yadda barin bari yagano hakan ba da kansa kuma. “No Sir I can’t marry you, I can’t dan Allah kabar wannan magana, ni kawai release Ya Farouq.” “Yes, yes you will marry me Fannah Aleeyu. In ma tunani kike ko wani abu ze shiga tsakanin mu ki kwantar da hankalinki. *CONTRACT MARRIAGE* zamuyi.” “Contract marriage?” Ta tambayesa cike da rashin fahimta. “Yes contract marriage nima some weeks ago Abuu yace se nayi aure, seya aura min wata ‘yar uwarshi Falmata saboda yana ganin I’m still young wataran baran iya managing Enterprise d’ina ba kuma wai ban gama mallakin hankali na ba so yakeson yamin aure, nikuma nace masa barin aureta ba, mukayi deal dashi akan in 6 months time zan nemo mace in kawo masa gida wanda zan aura. Ni koda nan da infinity, k’arshen duniya za’a bani banga macen da zata min ba har inji ina sonta zan aureta ba, I will use you Miss Aleeyu and fake up a relationshop with you. Ni a rayuwa na banason aure, duk abinda ze had’ani da mace ma hasali banaso ke kad’ai ne...” Ya nisanta “when it comes to you I just don’t feel thesame way. Mu rufa wa junan mu asiri and help each other. Zan aureki for just *6 MONTHS TIME* after then semu rabu ince wa Abuu kinci amana na kin tafi kin barni, kince you don’t love me anymore, you see daga lokacin nan bare sake tak’ura na da zancen aure ba zece I’m broken I cannot move on kamar yadda shima har yau yakasa sake aure tunda Ummimi ta tafi ta barsa. Ke kuwa kinga nasan by 6 months time d’innan Farouq halan ya gaji da jira ya koma inda yafito kinga seki cigaba da tafiyar rayuwarki kamar yadda take da. Nikuma I promise you a k’arshen 6 months d’innan bayan munyi ending marriage d’in zan baki 6 million tunda dama contract marriage ne.” Ido sosai Fannah ta zaro 6 million???? Ta fad’i a ranta. “Kinga inma so kike kubar garin nan da family’nki zuwa wani garin zaku iya, yadda Farouq bare sake tak’ura muku ba. Kuma a kowani k’arshen wata zanna biyanki albashinki na aiki N500,000 sede bawai zakina min aiki bane still, zan sauk’e ki daga zama min PA, bareyi ace mata ta PA ta ba. I’ll get the papers ready gobe, all you have to do is sign them So what do you say?” Shiruu tayi dan tunanin ma ta kasa. Taya zatayi agreeing wa qudurin nan? Contract marriage, how? Setayi decieving kowa kenan tasa su yarda eh soyayya sukayi da Mr. Fauzi har ya kai ga aure? Kuma seya b’ata mata image gun iyayensa, yace taci amanar sa? Gaskia baratayi ba amman kuma intayi la’akari itace ma zata fi benefiting. Dubu d’ari biyar sau 6 miliyan uku kenan plus miliyan shida daze bata ta tashi da miliyan tara kenan. Wow! Zata samu takai Babanta har k’asar waje ayi masa aiki takuma tattara family’nta subar Maiduguri su koma ko Kano ko Kaduna inda su Farouq bara su sake saminsu ba. Zata samu ta sa Afrah ma a makaranta. To yanzu ya? Ta yarda kenan? “Miss Aleeyu?” Ya tsamota daga cikin duniyar tunanin data wula. “Have you make up your mind?” “Sir naji komai amman seka b’ata min image gaban iyayenka ne su d’au mutumiyar banza ce ni?” “Yes Miss Aleeyu this is the only way zan kub’uta, the only way Abuu zeji tausayi na bare sake min maganar aure ba har se in ni na masa.” Kai ta gyad’a a hankali “Sir amman baramu na had’a kwanciya bako?” Lallai ma yace a ransa, shi d’inda ko wace mace nada burin ganinsa kan gadonta ita tasamu zata tsaya tana masa tsiya. “Miss Aleeyu nima ba so nake ba dan yazama dole ne, ofcourse we will share a bed amman ba abinda ze shiga tsakanin mu, in ma gudun abinda kike kenan, kisani banida interest cikin wancan abin ko physical contact ban yarda ba, lokacin da zamu iya tab’a juna shine only if either your family or my family visits saboda kar su gane faking auren mukeyi.” “Sir you mean barin sanar da su Mami ba? Ai ya kamatasu su sani-” “Bekamata ba” ya katse ta. “Ko Afrah ban yarda ki fad’a mata ba, this is our secret dan the moment kika sanar da mutum d’aya kin mana ruining komai kenan. Don’t tell anyone, clear?” Kai ta gyad’a tana nazarin ya zata soma b’ullo wa family’nta da wannan zancen auren Mr. Fauzi. Ai se suce dama tuni soayyaya ke kai ta office nasa ba aiki ba. “Good” yace. “So starting today zakiyi faking zama girl friend d’ina saboda kar mutane suyi suspecting relationship namun bana gaskia bane.” “Is that necessary Sir? Senayi pretending zama girlfriend naka a idan mutane?” “Yes Miss Aleeyu kidena san abu kina kaiwa kasuwa, bakiya san zama girlfriend d’inan ne? Sure kinaso so stop pretending and let urself celebrate.” “No ni banaso” ta kare kanta. Wani shu’umin murmushi ya saki mata. “In ma saboda Yusuf saurayin kine kike wannan abu gwamma tun wuri ki bari, kije kiyi breaking up dashi dawuri dan baraki b’ata min reputation ba ace kina dating d’ina kuma kina dating me aiki k’ark’ashi na ba.” “Sir Yusuf ba saurayi na bane.” “Allah sa” yace ba tare da ya nuna danuwa ba. “So ki bud’e kunnwanki da kyau ki jini, akwai rules da zan kafa miki regarding wannan aure;. Na farko shine don’t fall for me, saboda fake relationship ne I will show you love and care amman kisani bana tsakani da Allah bane, so in kika yi falling min ba ruwa na ke zaki karya wa kanki zuciya dan ni ba sanki zanyi in return ba.” Dad’in abin ba yau ta soma jin munanan kalamunsa ba so ko damuwa batai ba. “Ka kwantar da hankalinka Sir ni barin tab’a falling maka ba, business is business” “Allah sa ki iya ignoring beauty na. Na biyu we will be hanging out tare, duk inda zanje tare zamuna zuwa irin su dinner ko lunch da ake inviting d’ina so as inyi introducing naki wa bussiness colluegues d’ina. Inada business trip nan da 1 month da 2 weeks zuwa Morocco dake zanje. Na uku, I will re transform you, you are now my girlfriend ya kamata ki fara sa kayaki masu tsada saboda mu nuna wa public kin kai ince ina sonki.” Wannan wace erin zagi ne? Meyake nufi? Kaya masu arha take sawa kenan ko meh? Baki ta bud’e zata masa gana. Ya dakatar da ita ta hanyan aza hannunsa kan lips nasa “shh! Bangama ba karki katse ni. I know kinasan kice you are not ashamed, if you are not toh ni I am and that stays that. Hope am clear for now, more rules will follow afterwards...” *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:53, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 4⃣7⃣ “Baki jini bane?” Ya tambayeta tare da d’age gira. “Naji Sir” ta amsa a hankali. “Good and one more thing, learn to call me Anas in public. Bareyi kina kiran boyfriend naki sir ko Mr. ba. Am I clear?” Wani banbarak’wai maganganunsa suka sauk’a a kunnenta, ita rabuwan ta data kira sa da asalin sunan sa tun kafin ta fara masa aiki ta riga ta saba da Boss ko Sir ko Mr. Fauzi. “But Sir na riga na saba.” ta fad’a. “Seki saba da Anas d’in shima. Yanzu rufo min k’ofar mota.” Ba gardama ta rufe, basu tsaya ko ina ba se babban shopping mall dake Maiduguri bayan yayi parking ya juyo ya kalleta kallonsan take itama amman take ta kau da kanta. “So kinga cikin mutane zamu shiga am now your boyfriend dan haka karki kirani da wani suna banda Anas, clear?” Kai ta giad’a a hankali. “Me zamuyi anan amma?” Ta tanbayesa. “What else? To shop for you.” Ta kai da bud’e k’ofarta kenan ya dakatar da ita “wait, I’m your boyfriend ko kin manta ne? Let me.” Hannunta ta mayar tana jiransa bayan minti d’aya k’ofarta ya bud’u. Hannunsa ya mik’o mata a yayinda ta tsaya tana kallansa dan bata san me zata masa ba. “Grab my hand” yace da ita romantically. “Sir-” kallo ya watsa mata “I mean Anas kai fa kace ba body contact.” “If we are alone ba, yanzu kuma cikin mutane zamu shiga we have to pretend like other lovers do, now grab my hand.” “Sir I mean Anas amman haramun ne ba kyau, you are not yet my husba-” bata k’are maganar ba yakama hannunta tare da fito da ita daga motar. Janta ya fara suna tafiya se k’ok’arin k’watan hannunta take takasa, bece mata komai ba sanda suka iso daidai gaban k’ofar ya tsaya ya kalleta. Chak itama ta tsaida damben k’watan hannun ta datake kanta a sunkuye. “Fannah” ya kira sunanta abinda be tab’a yi a gabanta ba. “Stop it okay? Behave yourself.” A haka suka shiga cikin mall d’in idanu ne sosai akansu dan ko ba’a tab’a ganin Mr. Fauzi da mace ba segashi yau da PA’rsa. Wani business colleague nasa ne dayazo shopping shima da family’nsa ya gansa. “Mr. Fauzi” ya danna masa kira from far behind atare Fannah da Anas suka juya suna kallon inda suka jiyo muryar. Anas na ganinsa yakira sunansa shima “hey Mr. Mahmoud!” bayan Mr. Mahmoud sun k’ariso da matarsa sukayi hand shake sannan akayi gaisuwa. “This is Miss Aleeyu your PA ko?” Mr. Mahmoud ya tambaya. “Yes this is Fanna” ya sake rik’o hannunta gam da nasa yana mirzawa a hankali, electric sparks Fannah tajiyo cikin jikinta. “My girlfriend.” “Your girlfriend?” Mr. Mahmoud ya nanata abinda Anas ya fad’i cike da mamaki a iya saninsa de Anas baida time na girlfriends. “Yes!” Anas ya jaddada masa, “she is no more my PA right *BABE?* ” Ya juyo yana kallon Fannah. Rasa na cewa tayi chan k’asa k’asa cike da kunya tace, “yy..yyess” ta nisanta “honey ” Wani shu’umin murmushi Anas ya saki. “So Mr. And Mrs. Mahmoud semun sake had’uwa girlfriend ita tanada gajan hak’uri kar mu b’ata mata lokaci se anjima.” “Ayi shopping lafiya Mr. And Mrs Fauzi.” A haka sukayi sallama, hannunta rik’e cikin nasa suka nufa wajen inner wears. Me kuma zamuyi anan? ta tambayi kanta a zuci. Me kula kayan wajen tana ganin Mr. Fauzi ta soma washe hak’wara “Mr. Fauzi you’re welcome have a sit please.” “No thanks” yace mata tare da k’arisowa gabanta da hannun Fannah cikin nasa. “Dubata wani size ne ze mata.” Baki wangalau Fannah ta bud’e cike da mamaki da kunya gabad’ai wai mesa Mr. Fauzi baida kunya ne? Hijabinta ta hura sede its too late matar ta riga tayi figuring out komai. “Lets say maxi B cup.” “Okay thanks” yace da ita tare da jan hannun Fannah suka shige ciki, wajen bra zalla ya kaita bi yake yana duba tags na jikin bras d’in har ya kai kan tag B hannunsa ya raba da nata tare da d’iban bras d’in ba iyaka ya jibge mata ajiki, da sauri ta tare a hijabinta. “Sir I mean Anas meh haka? Its embarrasing dan Allah ka bari.” “What so embarrasing Fannah? You are my girlfriend me aciki dan na saya miki inner wears?” Wani sabon row ya kwasa ya sake zuba mata cikin hijabinta. Janta yayi zuwa side na panties yana duddubawa chan ya d’aga guda d’aya yana duddubawa a sama “Mr. Fauzi I mean Anas dan Allah kabari kar a ganka.” Banza yayi da ita tare da ajiyewa, wani daban ya sake d’agawa shima da be masa ba ya sake d’ago wani. “Saboda Allah Mr. Fauzi kabari.” “I won’t stop se kin fad’a min size naki.” “NOO!!” ta fad’a da ihu. “Then fine haka zan cigana da nema har sena samu.” Haka yatayi har wucewa ake ana nuna su. Ganin ba mahalicci se Allah ta rufe ido kawai “Sir size na hannun kan ne.” Juyowa yayi kalle ta dawani shu’umin murmushi a fuskarsa. “Good” ya ce da ita kalan size d’in ya riga d’iba har rows uku ganin kayakin sun soma mata yawa ya buk’aci akawo masu trolley dam ya cika d’aya da inner wears zalla sekace kayan lefe ze had’a. “Anas ya isa please ina zan kai wad’annan kayaki?” “Basu miki bane akawo wasu desingers d’in daban?” “NOOO MR. FAUZI!!!” Ta masa ihu, trolley’n yaja tare da rik’e hannunta wajen biya suka nufa ya ajiye tare da jawo wani trolley’n daban. Siyayya na fitan hankali yayi wa Fannah tun tana yabari har tagaji, shi kansa be bari taji total amout d’in ba. Har gaban gida ya kaita yasa yara suka shiga da kayakin ciki. “So are you telling Mami ko in shiga in fad’a mata da kaina?” “Zan fad’a mata da kaina.” “Yaushe yanzu?” “A’a se in bikin ya kusa.” “Kina nufin har se na gama gina gidan tukunnah?” “Yes Sir.” “Lallai kam!” yayi exclaiming. K’ofarsa ya bud’e yafita tare da bud’o nata. Hannunta yaja ya fito da ita sannan yasoma janta zuwa cikin gidansu. “Mr. Fauzi dan Allah kar ka shiga zan fad’a mata da kaina.” “When gobe jibi? I don’t have that time.” Already su Mami suna tsaye jikin kayakin duk mamaki ne d’auke karara a fuskarsu da Afrah harda Aiman. “Laaaa Mami kiga harda bressier” cewar Aiman. D’aya taciro “kuma wallahi daidai dana ya Fannah ne ko Ya Afrah.” Daidai lokacin su Anas suka iso tsakar gidan bra d’in Mami ta amsa tare da b’oye wa a bayanta ganin Mr. Fauzi. “Sannu dazuwa” ta musu duka. Bayan an shimfid’a musu tabarma suka zazzauna, sede Anas yak’i sakin hijabin Fannah dan dolenta ta zauna kusa dashi. Mamaki ne yacika Mami, Afrah kam gani take kamar a mafarki. Gyaran murya Anas yayi; “Ermmm Mami you must be wondering me ya kawo ni nan as well as kayakin chan ko? Well Fannah and I have been wanting to tell you amman Allah be bamu iko ba.” Ya juya ya kalli Fannah tare da mata wani killer smile dataji zuciyarta na k’ok’arin fashewa dak’yar ta iya ta mayar masa da murmushin itama. “We two... We two...” Sekuma yakasa k’arisawa nanne Mami tagano bakin zaren. “Ya Anas soyayya kuke da Ya Fannah?” Aiman ta tambaya, bakinta Mami ta buge “tashi kishiga ciki.” “Mami nayi shiru.” “Tashi nace!” Mami ta bud’e mata ido, a sanyaye ta tashi tashiga d’akin Baba. “Toh Anas shine har se kai da kanka zakazo ka fad’a min? Ke Fannah meya hanaki fad’a min iyyeh?” Kame kame ta soma “erm.. Erm...” Anas ne ya karb’eta “Mami ni na hanata saboda nayi laifi nafara soayyaya da ‘yarku ban tambayi izini wajen ki ko Baba ba, I’m sorry please.” “Bakomai Anas nasan bada gangan kayi hakan ba, toh inde blessing d’ina kuka zo nema ni kam na baku, Allah sanya alheri, naji muku dad’i sosai.” “Mungode Mami” cewar Anas a kunyace. “Yau ma Baba yana bacci ne inasan mu gaisa.” ya tambaya cike da girmamawa. “A’a idansa biyu barin masa magana” nan ta fice. “Congratulations to you two” cewar Afrah. Kallo Fannah ta watsa mata a yayinda Anas yace, “thank you sistaaa.” “Toh Ya Anas, Fannah kad’ai aka sani aka ma siyayya mufa?” “Ke Afrah bakida hankali ne?” Cewar Fannah tana zaro mata ido. “Toh ke me ruwanki?” Anas ya katse ta “don’t worry Afrah” hannu yasa cikin aljihunsa yaciro bundle na d’ari tare da mik’a mata. “Gashi gobe keda Aiman kuje kuyi shopping kinji? In ya kasa muku ki karb’i number na wajen Fannah ki kirani se in k’ara muku kinji?” “Yeyy! Ya Anas mungode.” Daidai da fitowar Mami kenan “bismillah Anas kashigo” a hankali ya saki hijabin Fannah tare da mik’ewa ya nufa d’akin. “Ya Fannah ya akayi Ya Anas yasan size naki naga harda bressier ya sayamiki.” “Afrah wallahi in baki rufa min baki ba sena cicci miki.” “Uuuhhh! Kode harda panties ne? Soyayya dad’i” hannu Fannah ta d’aga zata bugeta take ta gudu d’akinsu wane ta cinye kud’in. Bada dad’ewa ba Anas ya fito murmushin dake d’auke a fuskarsa kad’ai amsa ne game da tambayan ya had’uwansa da Baba ya tafi, it was a success. Mami ce ta rakosa waje “toh Anas kaide kullum seka mana wahala mungode Allah saka da alheri ya k’ara bud’i.” “Ameen Mami ni zan wuce.” “Toh masha Allah Fannah baraki raka Anas nakin bane?” Mami ta tambayeta tana mata murmushin tsiya. Kamar tace barin raka sa ba sekuma ta fasa tace “zan raka sa Mami.” “Yawwa toh mungode ko Anas a gaida gida.” A sanyaye ta mik’e ta bi bayansa bayan sun fito gaban gidansu yace da ita “toh Mrs. Fauzi thank you koma ciki.” “Niba Mrs Fauzi bace tunda ba’ayi auren ba tukuna.” “Ohonki nide adena so ana kaiwa kasuwa. Cikin jakar inner wears d’in akoi kud’in d’inki ciki also akwai wani paper da phone number rubuce ajiki, number’n tailor’n Amal ne naga yana k’ok’rin d’inki seki kirasa kuyi magana, okay?” Can k’asa k’asa tace “okay nagode” tare da ficewa. Tana dawowa taga su Afrah kan kayan se bud’e bud’e sukeyi. Sanda ta ganta sannan ta soma maganar; “ai dama Mami na fad’a miki akoi b’oyayyen al'amari tsakanin Ya Fannah da Ya Anas bakiga kullum tana zuwa office ba.” Yi tayi kamar bata jita ba takai da shiga d’akinsu kenan Mami ta kira sunanta “Fannah! tsaya” chak ta tsaya. Mami ce ta k’ariso wajen ta “mu shiga daga ciki.” Bayan sun shiga suka zauna kan gado Mami tasa hannunta cikin na Fannah. “Fannah shin kin sanar da Anas labarinki kuwa? Banasan ku gina relationship kan k’arya ki fad’a masa komai akanki please dukda da k’yar ne agane wani d’a na miji ya tab’a shiganki amman yakamata ki sanar dashi, k’arya ba abar yi bace.” Rasa na fad’i tayi. “Fannah Habibti kinyi shiru ko baki fad’a masa bane?” Qarya ta mata; “ko kad’an Mami, karki damu na sanar dashi komai ahakan kuma yace yana sona ze aureni, ya kuma buk’ace ni da kar in sake kawo masa zancen koda wasa same goes to you to please Mami, maganan ya wuce kar mu sake d’agowa.” “Toh Alhamdulillah na matuk’ar jin dad’i wallahi, mahak’urci mawadaci kinga amfanin hak’uri kenan. Yanzu koda Ya Khaleel ya dawo se mu fad’a masa kinada mijin da zaki aura.” “Mami Baffah Khaleel ma bare sake dawowa ba sabida a yanzu haka Ya Farouq yana cell...” nan ta labarta wa Mami komai. Ba abinda Mami ke inbanda sunbud’a wa Anas albarka. **** Shima Anas d’in daga gidansu Fannah gida ya zarce cinye sa ne kawai su Ummie basuyi ba dan murnan ganinsa da sukayi. Abuu, Shettima kowa yaji dad’in ganinsa. Bayan sun gama cin abinci ya dawo d’akinsa ya jinguna jikin gado, besan dalili ba kawai ya tsinci kansa cikin nishad’i da jin dad’i musamman inya tuna reaction na Fannah data fad’a masa size na panties nata. Knock ne yazo daga k’ofar sa. “Come” yace. Shettima ne yashigo ya nemi waje ya zauna kusa dashi. “So Ya Anas ina kashiga kwana biyu ka kusan sama Ummie hawan jini Amal kuma ciwon hauka?” “Nowhere maza just that I needed space to think.” “Sure?” Ya tamabayesa yana wani murmushin tsiya. “Yau kuma dawani surutun ka taho?” Ya tambayesa. Well d’azu aka kirani w“ai an ganga a mall kai da Fannah kuna shopping.” “Mutane da gulma!” abinda yace kenan. “Aww dagaske ne kenan?” “Nima ban sani ba” ya amsa sa a takaice. “Tashi ka fita ma please don’t ruin my day. Nifa na fad’a maka ba san Fannah nake ba I’m just using her and thats all.” “Toh in tayi tsami mua ji nide a dage ko weekend ne a kawo mana ita muyi spedning.” Pillow Anas ya d’aga ya wulla masa wanda Shettima yasamu yayi dodging ya fice a guje yana dariya. Shikansa Anas dariyan yake. ***** Da tunanin Fannah wanda keson zama masa jiki yayi bacci. Sede mafarkin Ummimi daya kwan biyu beyi ba yayi yau. A firgice ya tashi yana gumi yana nishi, k’ark’ashin gadonsa inda yake adana bottle d’aya zuwa biyu saboda situations like this in yayi mafarki yasha ya d’au d’aya ya bud’e. Har ya kai baki sekuma ya kasa sha yayi promsing Fannah bare sake sha ba, rufewa yayi. Wata zuciyar tace masa toh ai ko kasha barata sani ba tunda ba ganinka take ba. Nan ya bud’e ya sake kai baki nan ma yakasa sha. “Oh God! NO!!!” Toilet ya nufa ya juye a bathroom yayi flushing haka yayi da d’ayan ma, sannan ya koma ya kwanta. Ina fa, bacci ya gagara, mafarkin Ummimi se hunting nasa yake. Wayarsa ya d’ago daga kan side drawer yaga k’arfe 1:20AM. Miyarwa yayi ya sake kwanciya daga ya rufe ido se mafarkin Ummimi ya dawo daga inda ya tsaya. Yayi hakan sau uku kawai ya hak’ura da baccin inda giyansa na nan da yana sha nan da ‘yan mintuna zeyi everlasting bacci, duk laifin Fannah ne ita tasa sa yayi making promise kan bare sake shaye shaye ba, yanzu haka ita tana bacci shi yana nan yana wahala sede ayi 2-0. Wayarsa ya sake d’agowa yaga 1:40AM kan lambarta yakai ya danna mata kira. **** Fannah na cikin baccinta me dad’in bala’i tajiyo ringing na wayarta ita tama rasa meya hanata sawa a silent har yagama ringing bata d’aga ba se a karo na biyu. Cikin bacci ta d’aga “hello” dan ko duba wake kira batai ba. “Miss Aleeyu” ya kira sunanta ai take ta nemi baccin nata ta rasa. “Mr. Fauzi”,takira sunan sa cike da mamaki. “Me ya faru da daren nan?” Torchi ta haska taga k’arfe d’aya ne. “I can’t sleep” yace da ita sincerely. “Toh Mr. Fauzi nikuma me zan maka?” “Nima bansani ba all I know is that is your fault.” Hamma ta saki tare da zaro idanu “nikuma Sir? Mena maka?” “You made me promised to you that barin sake shan wani abu ba, I’m badly in need of that now kuma na kasa sha, because I can’t break my promise to you!” ya fad’a ad’an tsawace. “Is okay calm down Mr. Fauzi, calm down okay? Karka sha please, zaka iya tashi zuwa kitchen?” ta tambayesa a hankali cikin murya me sanyi. “Yes” yace mata. “Good you are going to make your coffee, trust me in kasha you’ll go back to sleep peacefully but please kar ka sha wancan abun you promised, kaji Mr. Fauzi?” “Naji” yace tare da mik’ewa zuwa kitchen d’in. Haka tana fad’a masa directions d’in yana bi har ya had’a sede koda ya tab’a be kai nata dad’i ba. “It didn’t work Miss Aleeyu, ni barinsha ba.” “Yi hak’uri kasha, first thing gobe I’ll come to your office in had’a maka kaji? Yi hak’uri kasha wannan d’in please will you do that for me?” Shiru yayi bece komai ba “please” ta rok’esa. “Okay” ya fad’a can k’asa k’asa. “Sleep good okay? Gobe da safe zan zo in had’a maka coffeen kaji?” “Naji” yace karap ta katse wayar. Da k’yar ya iya shanye rabin coffeen. Kasancewar ba Fannah ce ta had’a masa ba, sam ya kasa bacci amman dan yadda muryarta ke yawo masa a kai besan lokacin daya koma bacci ba. *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:53, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 5⃣1⃣ Nishi take sosai tana hak’i a yayinda zuciyarta ke bugawa d’ari bisa d’ari, ko damuwa ta kewayo dan ganin ya cikin gidansu Anas yake bataiba, abinda tasani kawai gidan nada kyau, bayan ta tabbata dawakan sun wuce tagwada bud’e k’ofar daidai lokacin Shettima ke dawowa daga yawonsa shima a tare suka tura k’ofar sede ya rigata. Suna had’a ido ya sakar mata da murmushi, murmushin ta mayar masa sede daga yadda take abu yagano tana cikin hanzari. “Fannah!” “Na’am Shettima.” Ta amsa. “Yau kece a gidan namu?” Ya tambaya yana mata murmushi. “A’a dawakai suka biyo ni, ina jiran Anas ne barin wuce please.” Ta fad’a cikin hanzari duk hankalinta ba’a kwance ba. “Fannah lafiya?” ya tambaya tare da sake blocking nata. “Shettima please ka matsa min in fice, kar Anas yaganni anan.” “Ya Anas? Shi yace karki shigo ne?” Shiru ta masa bata amsa ba hakan ya tabbatar masa da ‘eh’ ne amsar. “Karki kula sa haka yake shigo please kinji? Amal tayi missing naki.” “A’a Shettima, wataran zan dawo amman yanzu ka matsa min in fice please.” ta fad’a tana duba bayanta gudun kar Mr. Fauzi yaganta. “Haba mana Fannah yanzu baraki shigo ba? Yi hak’uri, Ummie naciki kinga seku gaisa kinji ko bahaka ba?” Kai ta girgiza masa tana tuna irin warning da Mr. Fauzi ya mata. “A’a I promise next time amman yanzu wallahi nashiga Anas ze sab’a min.” “Trust me ba abinda ze miki shi Ya Anas haka yake, sharesa please kishigo.” Nan ma kai ta kad’a “please mana Fannah sena had’aki da Allah ne? Kishigo please.” “Shettima wallahi Anas yace kar in shiga, kabari next time.” Kafad’a ya buga “ai wallahi sekin shiga Fannah, mubar musu kawai kinji? Bismillah.” “Shettima please...” Kai ya girgiza mata ganin ba mahalicci se Allah tace, “Shettima inyamin masifa fah? Seda yace min kar inshiga fa.” “Ai sharesa zakiyi, haka yake mushiga please.” A sanyaye tabi bayansa duk tsoro yabi ya ratsa ta tunanin wani erin masifa zata sha wurin Mr. Fauzi kawai take, sun kusa da bakin k’ofar ganin Shettima bai ganinta taja da baya zata gudu aiko tuni yaganta ta jikin mirron window karap ya cafko abayanta. “Fannah aini ba’a min wayo, mushiga kawai.” “Shettima kayi hak’uri please kabarni in tafi.” “Mushiga kawai Fannarmu.” Haka suka shiga cikin katafaren parlour’n su, dake d’auke da kayan tafiyar da imanin mutum a kowani second. Zaune ta iske Anas da Ummie kan kujera. Bayansa ta hango saboda kallon direction na Ummie dayake. A lokacin da idanunsu ya had’u da Ummie kuwa tayi saurin sunkuyar da kanta. “Shettima!” Ummie ta kira sunansa cike da mamaki ganinsa da budurwa. “Yau kuma budurwarka ka kataho mana da ita gida?” Jin an ambaci budurwa Anas ya juyo dan ganin wannan budurwar Shettiman yayi dariya. Ai zubewa ne kawai idanunsa basuyi ba a k’asa dan yadda ya warwarosu ganin FANNAH a parlour’nsu. Inba wai ya manta bane he made it clear to her karta kuskura tashigo. K’in d’ago kanta tayi su had’a ido tinda taji alamun blue eyes nasa a kanta. Yafi minti d’aya yana kallonta totally speechless bema san me zece mata ba dan yadda tabasa mamaki. “A’a Ummie ai wannan tafi k’arfina zubin billonaires ne da ita” cewar Shettima har yanzu Anas bebar kallon Fannah ba launin fuskarsa take ya koma ja dan b’acin rai ko sauraron Shettima ma beyi ba. “Dade Ya Anas kika tambaya bare rasa amsar da kike nema ba.” Se yanzu hankalinsa yadawo, kallon Shettima yake tare da watsa masa wani irin wawan kallo. “Kai Shettima deh!” Cewar Ummie cike da zumud’i. “Fannah ga Ummie, Ummie ga Fannah.” Shettima yayi introducing nasu wa juna. Har k’asa Fannah ta tsuguna ta gaishe da Ummie cike da girmamawa, itama Ummien cike da fara’a ta amsa ta. “Taso ‘yata taso dan Allah” kafin ace meh Ummie taje ta r’iko Fannah tare da k’ariso da ita kan kujeran da suke zaune da Anas, a yayinda ta zauna kan hannun kujerar irakuma se kallon Fannah take kamar ta cinye ta, Fannah kuwa fitsari ne ya matse lokaci d’aya dan har yanzu Anas bebar kallonta ba. “Shettima kace wannan kyakkyawar ba budurwarka bace?” “A’a Ummie, Ya Anas kama Ummie explaining mana.” Kallonsa yadawo gare da Shettima, “wallahi inbaka min shiru anan ba zan maka duka.” “Kai Ya Anas a gabantan ma bara muyi koda shirin k’arya ba? Ai ganga ake bugi ba mutum ba. Zaka fad’awa Ummie wace ita ne ko in fad’a mata.” Takalmin k’afarsa yayi yunk’urin cirewa, Shettima na ganin haka ya lab’e bayan labule. “Fannah koh?” Ummie ta tambaya a nitse. “Eh Ummie” ta amsa ta cikin siriryar muryarta. “Toh Masha Allah ke da wa kuka shigo?” A hankali ta d’aga kai ta kalli Anas da ba abinda yake in banda hararan dayake watsa mata, miyau ta had’iye takasa amsa tambayar Ummie duk tsoro ya cika ta. “Ita da Ya Anas ne” cewar Shettima dake lab’e bayan labule. “Wai Ummie ke baki gane bane? Budurwar Ya Anas ce fah.” Ido gam Fannah ta matse tana niran sauk’an duka. “Budurwarsa fa kace Shettima? Alhamdulillah!” Rungumo Fannah tayi, se mammatse ta take a jikinta. Anas ji yake kamar ya k’urma ihu dan takaici da bak’in ciki. “Ashe Allah ze nuna min ranan da Babana ze kawo min mace gida, kai alhamdulillah. Fannah tunba yau ba nake jirar wannan rana, ranarvda zamu had’u. Allah miki albarka, kai nagode. Kinga sekina hak’uri da Baban nawa sabo-” bata k’are maganar ba Anas ya katse ta. “Wai me haka Ummie? Nifa ba budurwa ta bace, tsiyar Shettima ne kawai, ke tashi mu tafi.” Yace da Fannah alokacin daya dawo da kallonsa gareta yana galla mata wani erin harara. “Baba na meyayi zafi? Ai wannan ba abar b’oyewa bace iyyeh? Ko rowarta kake mana ne?” Shafo fuskar Fannah tayi “ ‘yata karki jisa kinji? Yi zaman ki.” Cike da kunya da tsoro tace, “uhm Ummie ba buduwarsa ce ni ba, wasa Shettima ke miki.” Da murmushi sosai a fuakarta tace “ni nagane ‘yata, Allah barmin ku tare. Barin kawo miki koda ruwa kinji?” “Wai Ummie meh haka ne? Kekuma tashi mutafi.” Anas ya fad’i a fusace. “Ba inda zataje, Shettima duba ko Abuu na gida ka masa magana.” “A’a Ummie karki damu please-” Fannah bata k’are maganar ba Ummie ta katse ta “ ‘yata karkiji komai kinji? Feel free, feel at home. Jeka duba Abuu Shettima.” Nan ta fice kitchen a yayinda Shettima yaje duban ko Abuu na gida shima, yarage daga Fannah se Anas. Hannunta ya kama tare da murd’awa cike da mugunta. K’ara ta saki “arghh! Mr. Fauzi please ka sake min hannu da zafi.” take hawaye ya soma cikowa a idanta. “Da zafi? Me nace miki amma, didn’t I tell you kar ki shigo? Mesa bakiya jin magana ne?” Azaban ne yamata k’ak’a har hawayen suka soma tsiyaya dan yadda ya murd’a hannun nata. Daidai nan Ummie tafito da tray cike da snacks da drinks akai. “Ya meke faruwa?” ta tambaya alokacin datake k’arisowa cikin parlour’n. Hannun Fannah ya sake da wuri gudun kar Ummie tayi suspecting wani abu amman ina ta riga ta hango hawayen dake mak’ale cikin idanun Fannah. “Ya Salam Mama na meya sameki?” “Bakomai Ummie abu ne yashiga mata ido.” Anas ya amsa tun kafin Fannah da aka tambaya tayi magana. “Sorry dear ya fita? Muga.” Kamar dagaske yawani sa hannu yana duban idanta harda hura mata iska. Hawayen ta had’iye “shikenan yafita” tare da kawar da kanta ba tare da ta kallesa ba. Serving nasu drinks d’in tayi. “Bismillah uwata” Ummie tace da Fannah. “Babana fad’amin mana toh ina kuka had’u da Fannah?” “Ummie please me haka ne? Fannah tashi mutafi.” “Yanzu Anas itanma se an mana rowanta?” K’arya ya mata, “Ummie we need to go ne, zan kawo ta some other day.” Dad’i sosai taji “ka yarda budurwarka ce kenan.” Ta fad’i dawani shu’umin murmushi tattare a fuskarta. Shiru yayi kamar be jitaba. “Anas fad’a min mana.” “Eh Ummie shikenan kinji? She is my girlfriend. Tashi mutafi Fannah.” Daidai lokacin Shettima ya dawo “Ummie Abuu fa bai gida kuma ga motarsa a pake.” Wani sanyi Anas yaji a ransa bashi kad’ai ba hatta Fannah dagajin Abuu bai gidah. Mik’ewa yayi itama haka, ko jiran tama Ummie se anjima beyi ba yasoma janta, itade Ummie cike da mamaki take kallon Anas budurwarsan ma bare saurara mata ba. Bayan sun shiga mota ya soma suburbud’a mata masifa wane an turoshi. “Wai ke mesa bakiya jin magana ne iyyeh? Didn’t I tell you karki kuskura ki shiga? You are not my girlfriend you are just a fake one banasan family na su ganki, kin huta ai yanzu da Ummie taganki mschww! Mutum ace mishi don’t amman seyayi.” Hawaye take sosai “Sir kad’au wai dagangan na shiga gidanku ne? Doki ne ya biyoni ta fad’i” cikin kuka tana share hawayenta. “I still don’t care!” Ya fad’a a tsawace. “Acikin motan me ze miki? Msschw! Kin d’au wasa nake ba, you’ll be suprised 1000 paper zan baki kiyi correcting.” Kukanta ne ya tsananta kamar ‘yar yarinya ta tsaya tana kuka harda me sauti tsuka yaja ya soma driving ganin kukan nata bana tsayawa bane ga kuma kukan ya soma damunsa ya tsaya gefe guda akan titi. Ko d’ago kai ma batai ba se kukanta da takeyi kanta cuse cikin cinyarta. “Toh kukan ya isa” ya fad’i a hankali. Banza tayi dashi ta cigaba. ‘Sorry’ yakeson fad’a mata amman bare iya ba, “ya isa I shouldn’t have shout at you kinji? Stop crying” namma bata bar kukan ba. “Okay barakiyi correcting 1000 papers d’inba, I take that back, bar kukan.” Bata d’ago kai ba har a yanzun sede ta d’an rage kukan nata. “Bafa dan wai inaso bane na shiga gidan naku, doki har biyu ne suka biyoni ni nikuma inajin tsoro, dana shiga na had’u da Shettima, shine yayi insisting sena shiga.” Ta sanar dashi cikin sautin kuka. Sekuma yaji wani iri amman ai still da ta shiga koda gidan neighbours ne. “Toh d’ago fuskarki, kukan ya isa na fad’a miki banasan jin kukanki.” Tana d’ago kai ya mik’a mata hand kerchief nasa, amsa tayi ta share hawayenta a yayinda yayi zaman kallonta, kukanta na d’aya daga cikin abubuwan da yake burgesa a gareta, abu kad’an setayi kuka. Ice cream shop ya wuce da ita bata ce dashi komai ba. Bayan yayi parking yafito ya bud’e mata nata tare da rik’o mata hannu mutane kad’an suka samu ciki. Kap flavours dayasani na ice cream seda ya siye mata amman kuma bece mata nata bane haka suka dawo cikin motar, zaman makoki suka tayi har seda ya kawo ta gaban gidansu, a nitse ta bud’e k’ofar ko se anjiman ma batayi niyyan fad’a masa ba “girlfriend” ya kirata, banza tayi dashi da sauri ya cafko abayanta kafin ta rufo k’ofar. “Your ice cream take it.” “Banaso” tace tana turo bakinta, har yanzu haushi yake bata jibi yadda ya riga mata masifa. “Girlfriend take it kinji?” Hak’urin nan de dayakeson bata ne ya kasa. Ganin battada niyan d’aukawa yace, “okay barin sake miki masifa ba, kema obey all my rules yanzu d’auka kinji?” Wato shi be iya bama mutum hak’uri bako? Tace a ranta. “Ni ka sakemin abaya in tafi.” “Fannah” yakira sunanta yadda takeso “take it kinji? Barin k’ara ba.” Kallonsa tayi na ‘yan seconds sannan ta ciro ledan tayi tafiyarta ko godiya babu. ★★★★★ “Ummie dan Allah Ya Fannah tazo?” Amal ta tambaya. “Eh kai!” Ummie ta amsata se dad’i takeji Anas yakawo budurwarsa gida. “Yace ze sake kawo mana ita karki damu.” “O’o ni barin yarda ba. Ni zanyi inviting nata birthday party na.” Daidai lokacin Anas yake sa kai cikin parlour’n da alama yajiyo abinda Amal tace just now. “Wa zakiyi inviting a birthday nakin?” “Ya Fannah mana Ya Anas shine ko ka fad’a min zaka kawota, amman ka iya cemin kar in fad’awa kowa picture’nta dake wayarka.” “Rangem! Ya zama fashashhen k’wai” cewar Shettima yana daka tsalle. “Ashe abin kenan, wayyo! Ya Anas ka nunwa Ummie mana taga hoton surikar tata.” Dafe baki Amal tayi batasan lokacin data fad’a ba. “Ya Anas I’m sorry wallahi bansan ya akayi na fad’a ba.” Wani irin kunya ne ya ratse Anas dayakeji kamar ya tone k’asa ya shiga ai yanzu shikenan sekowa ya zata eh son Fannah yake, bece da Amal komai ba illa k’arisowa cikin parlour’n da yayi a gaban Ummie ya tsuguna. “Ummie please kar kowa ya fad’awa Abuu yau wata ta shigo gidan nan.” Cike da mamaki Ummie ke kallonsa “toh Babana ai abu ne me kyau kuma shima dad’i zeji.” “A’a Ummie ni kawai kar kowa ya fad’a masa kaji Shettima?” “Senayi tunani tukun” yabasa amsa yana kallon yatsunsa dan tsiya. “Zan baka kud’i wallahi yanzu ma kaje ka d’auka bundle na d’ari biyu ni kawai kar ka fad’a masa.” Shettima lashe money najin haka yace “karka damu Ya Anas your secret is safe with me” take yayi d’akin Anas. Instead ya d’au na d’ari biyun seya zari na d’ari biyar dan kud’in suna nan ne ba adadi. Bayan yafito Anas yace, “muga nawa ka d’auka.” “Ji Ya Anas de baka yarda dani bane?” Wayarsa yaciro kamar ana kiransa. “Lecturan?” Yayi pretending yana kan waya. “Toh gani zuwa.” Aiko sauraran Anas beyi ba yafice shopping, yau za’ayi renewing wardrobe. **** “Ya Anas amman please ka amince inyi inviting nata birthday na ran monday, please Ya Anas.” “Eh mana Babana kabarta tazo kaji?” Ummie tasa baki. “A’a Ummie nikam kunga matsalar dayasa banso shigowar yarinyan nan ba kenan.” “Toh meh aciki? Ai wallahi ko ka yarda ko in fad’awa Abuu yaso nan da wata ma ayi bikinn mu huta, in tanada k’anne ma duk su taho tare.” “A’a please na yarda zan fad’a mata ni kawai karku fad’awa Abuu. Ita kad’aice batada k’anne.” “Ya Anas amman fa akoi wata Aiman da muka tab’a gaisawa da ita.” Kunya yaji an kamasa yana k’arya. Wani kallo Ummie take masa ina irin angano kan nan. “Toh meh? Ai ba k’arya nayi ba na mance ne.” Nan ya tashi yashiga d’akinsa se huci yake shi ya tsani abunsa haka. Yanzu what if Abuu ya had’u da Fannah kuma fah? Mschww! Wayarsa ya zaro daga pocket nasa ya danna mata kira alokacin kuwa ita dasu Aiman da Afrah duka suna zaune suna shan ice cream nasu. Ganin shi ke kira tak’i d’agawa halan wani masifan yakeson mata. Seda yakusan tsinkewa ta d’aga “hello” tace a hankali, Afrah kam ko kyafta ido battayi dan gulma ganin haka Fannah ta bar musu d’akin. “Kin iya shiga gidanmu ba? Ai gashi yanzu Amal tace sekinzo birthday’n ta ranan monday mutum ace masa don’t amman se yayi.” “Birthday’n Amal? Toh Sir kace musu zanyi tafiya mana ai ba lalle ne senaje ba tunda baka so.” “You should have thought about that ai kafin kika shiga, daman abinda kikeso kenan kisamu kina shigan affairs na family na.” “Ni ba abinda nakeso ba kenan kuma barinje ba, shikenan?” “Miss Aleeyu don’t dare me, Monday by 4:00PM driver zezo ya d’aukeku dasu Afrah duka inform them, ni na fad’a miki” karap ya katse. Harara ta watsa wa wayar wane shine Anas d’in. Bayan takoma ciki tabasu Afrah labari ai ice cream da ba’a gama sha ba kenan dan dad’i. Kayan wardrobe nata ta zazzage duka ana neman kayan zuwa party ganin ba wanda ya gameta ta yafo mayafinta suka fice shopping da Aiman. *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:54, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 5⃣2⃣ English wears had’ad’d’u na ‘yan gayu maras tsireci ta siya wa kanta sannan wani had’ad’de wa Aiman itama bata damu da Fannah ba saboda tasan bara’a rasa d’aya cikin kayakin da Anas ya siya mata ba. _2 days later..._ _Monday 3:30PM_ Kaya ne wargaje cikin d’akinsu Fannah, su Afrah ana shirin zuwa party. Ba hassada tayi kyau, kayan ya mata kyau makeup nata yayi kyau, kamar yadda ta tsara kanta haka ta tsara Aiman ma dukansu biyu sunyi kyau banda Fannah dake zaune kan gado tana buga candy crush da towel d’aure a k’irjinta. “Wai Ya Fannah bara kije bane? Dubi time fa! Ga kayanki nan tun d’azu na cire miki kink’i sawa.” Cewar Afrah “Barin jeba in kun had’u kice masa banida lafiya.” Daidai da shigowar Mami kenan “waye ne baida lafiyan?” “Mami wallahi gatanan tak’i tashi ta shirya.” “Mami wallahi k’arya take, yanzu fitowa na daga wanka ko Aiman? Ina kayan nawa insa. Wane ni ace birthday na in-law na barinje ba.† Kallonta Afrah ke cike da mamaki. Kayan ta jawo ta zira wata maroon doguwar riga ne har k’asa me hannun vest da kwalya sosai a jikinsa ta saman, bayan tasa shi ta d’auko wata had’ad’d’iyar ash-ash jacket me siririyar dogon hannu dake shek’i ga kwalyan stones daya sha, yana nan da tsayi shima har kusan k’asa amman be gama kaiwa ba, ta d’aura akai. A bud’e yake saboda ya bayyano da kwalyan dake d’auke da doguwar rigar dake cikin. Afrah ce tamata makeup d’in basu d’au lokaci ba saboda ba wai gira za’a zana mata ba. Maroon gyale tayi rolling dashi seda ash jaka da takalmi data sa. Feffeshewa sukayi da turare 4:00PM on the dot driver’n yamata waya kan gashi nan. Allah kare Mami ta musu suka fice. Daidai gaban gidansu Anas ya tsaya bayan an bud’e gate ya shiga dasu. An k’ayata filin tsakar gidan da had’ad’d’en decoration na red and white, tsayuwa dan kwatanta kyan wajen ma b’ata lokaci ne. Bayan sun fiffito daga motar suka tsaya chak Afrah da Aiman kam se k’are wa gidan nasu Anas kallo suke bada jimawa ba gate ya bud’u motan Shettima ya bayyana. Yana ganin Fannah yaji wani dad’i ko lura dasu Afrah beyi ba seda ya fito suka gaisa da Fannah sannan idanunsa suka sauk’a kan Afrah (fire) kasa dena kallonta yayi dan had’ewar data masa, ashe ba Ya Anas kad’ai keda rabo ba harda nima ya fad’a a ransa. “Ina wuni?” ta gaishe sa. “Lafiya sannu ko? Fannah kuna kama ko sister kice?” “Eh sunanta Afrah wancan kuma Aiman.” “Wow pretty ladies sede ma Afrah duk tafi ku kyau.” “Noi! Wani kyau tafimu? Kwalya de ta fimu, nida Aiman duk munfita kyau.” “A ganinki kenan nide Afrah tafi min kyau.” Afrah kam se blushing take, wani me kama da Blue eyes yace mata tanada kyau. “Fannah kushiga daga ciki su Ummie suna parlour you all are welcome.† Duk wannan magana dayake yakasa d’aga idanunsa daga kan Afrah. “Tam, taho muje Aiman, Afrah lets go.” “A’a ni dakaina zan kai Afrah koban fad’a miki tafi ku kyau duka bane.” A hankali ta d’ago idanunta da suka sha tozali da liner ta azasu kan Shettima dake d’auke da murmushin dayake k’ara masa kyau, murmushin ta mayar masa, “lets go ko? My lady.,By the way I’m Shettima, k’anin Ya Anas amman fa karki d’au wani babban bro na ne, dududu shekara d’aya da rabi yabani.” Murmushi sosai Afrah ke harda ‘yan hakwara a waje. “Nima ai, 1½ years ne kawai tsakani na da Ya Fannah.” “Owww really? Zo mud’an fita kafin programme d’in ya fara.” Motarsa ya bud’e mata tashiga se rawan jiki yake yasamu ‘yar kyakkyawa. A ice cream shop ya tsaya suka sauk’a, kud’in Ya Anas zeyi amfani. Bayan an kawo musu ice cream d’in suka soma sha a hankali. Cikin d’an k’ank’anin lokaci suka saba sosai, dake halayensu na neman tsokana da neman zance duk d’aya ne, labarin abubuwan da suke ma yayunsu suka rigayi, bayan sun gama chan suka tab’o b’angaren karatu Shettima harda zuzutawa wai yana d’an business. Afrah ta jima tana nan perfect boyfriend segashi tasamu kyakkyawa k’anin billonaire. Ba b’ata lokaci Shettima ya fad’a mata santa yake, tunda idanunsa suka sauk’a kan kyakkyawar fuskarta yaji yana sonta. Aiko itama ma hakan ne, take sukayi exchanging I love you da I love you too. Bayan sun k’are shan ice cream d’in yakaita shopping duk acikin kud’in daya sata gun Anas ranan. Afrah kam dad’i kasheni. **** Fannah kuwa tun shigarsu gidan bata had’u da Anas ba taji Ummie na cewa baya gida ma, Abuu kuwa yayi tafiya, hamdala ta saki. Birthday girl ansha kyau sosai tana ganin Aiman taji tana san miyar da ita little sister tunda ita batada. Bada dad’ewa ba programme ya fara har a yanzu su Shettima masu soyayya basu dawo ba. Bada dad’ewa ba gate ya bud’u had’ad’d’iyar benz na Anas ya shigo. Bayan yayi parking yafito ko kallon direction na mutanen baiyi wajen Amal nasa ya nufa yayi wishing nata happy birthday tare da ajiye mata present nata na iphone 6+. Direct parlour ya nufa bayan yasha ruwa ya ciro wayarsa ya kira Fannah yaji ko sunzo. Tana zaune abinta taga call na Anas. Me kuma zece mata yanzu? Da k’yar ta d’aga “hello?” “Kunzo?” Ya tambayeta a takaice “Eh.” ta amsa sa. “Ina kike? Kizo parlour yanzu ina jiranki” karap ya katse. Inje kamin me ta tambayi kanta kamar wacce barata ba, sekuma ta mik’e taje zaune kan dining chair ta samesa ya aza k’afafunsa kan table d’in yana kad’awa da wayarsa rik’e hannunsa. Sosai shirin dayayi ya masa kyau kodan bata tab’a ganinsa da erin shirin bane? Shima kallon nata yake, gani yake kamar bata tab’a kyau erin na yau ba, kodan be tab’a ganinta cikin english wears bane? Kasa dena kallonta yayi, da k’yar ya iya cemata “zoki zauna” tare da ja mata kujeran gefensa. A sanyaye tanufa wajen sede bata zaunan ba gudun kar Ummie tazo ta kamasu bibbiyu. “Mr. Fauzi you called for me, wani abu ne? Kaga I need to get back.” “Sit toh.”,Yi tayi kamar bata ji saba. Hannunta ya rik’o “sit first.” Dan kawai ya sake mata hannu ne ta zauna. Bayam daya k’are mata kallo kusan na mintuna biyu yace, “kinyi kyau.” ‘Yar murmushi ta saki, “thank you.” Dad’inta kenan da Anas duk sanda tayi kyau ze fad’a mata. Cameran wayarsa ya shiga yayi muting, yasoma d’aukanta hoto seyi yake kamar amfani da wayar yake. “About business trip da zanje Morocco ne, nafasa zuwa dake tunda you are now my girlfriend, zamuje da Kacallah.” Dad’i sosai taji. “Okay Sir.” “Call me Anas.” “Okay Anas shikenan zan iya tafiya?” Besan meh ba seyaji bayason ta tafi yafison ya kasance tare da ita always. “Jibi ne tafiyan nayi rescheduling.” Nanma “okay” tace. So barata ce masa ko safe trip ko Allah kare ba wato. “What kind of an I don’t care girlfriend are you? I’ll be travelling ko d’an safe trip babu.” “Toh Sir nag-”,sekuma tayi shiru ganin battada abin cewa “I’m sorry, safe trip Allah ya kare ya dawo dakai lafiya.” Chan k’asa k’asa yace, “ameen seda na tambaya.” Ita Fannah bata aza abin boyfriend girlfriend nasun a ka ba saboda batasan ta sake bud’e zuciyarta ma wani na miji because a k’arshen ita zata wahala danko duk na mijin daya gano some day batada budurci ze guje ta, abinda bataso kenan, maganin bari kar ma a soma. “Zan tafi.”,Tace a hankali. “No I want you to stay Fannah don’t go.” Har a yanzu bebar d’aukanta hoton dayake tayi ba haka yak’i barinta ta tafi, kuma bawai hira yake janta dashi ba kallonta kawai yake yana d’aukanta hoto. Da kallon ya isheta tace, “Sir kaifa kace adena kallo dayawa.” “Yes amman ni ai am your boyfriend me aciki dan na kalleki? You also enjoy it when ever I’m starring at you so kidena pretending.” “Nima ai am your girlfriend amman dana kalleka sekace bakasan kallo, kayi adalci kenan?” “Miss Aleeyu kallon soyayya kikemin nikuma banaso, ni kawai kallonki nake saboda kinyi kyau.” “Toh nima ai saboda kayi kyau nake kallonka.” “Ni ai kullum inayin kyau, am handsome kekuma time-to-time kikeyin kyau.” Ganin inta sake magana ze iya zaginta tayi shiru kawai bata sake cewa komai ba k’arfe 5:30PM nayi ta mik’e “Sir zamu tafi kar Maghrib ya mana anan.” Hannun ta ya rik’o “I will take you guys home.” “No please karka damu we can go on our own.” “Fannah I’m your boyfriend I insist.” “Toh Mr. Fauzi kasakemin hannu please.” “No Fannah, I enjoy holding your hand, allow me.” “Sir ba kyau ne.” Kafin yace wani abu ta b’arke masa da kuka, shark’af shark’af besan lokacin da ya ciro hanky ya soma share mata hawayen nata ba. “Fannah why are you crying? Na miki wani abu ne? Kodan danace time-to-time kikeyin kyau? I don’t mean it kinji? You are beautiful, always looking gorgeous saisa nake kallonki kullum. Bar kukan kinji?” Har yanzun be sake mata hannun ba duk yabi ya kid’ime ganin yadda take kuka. Baya san ganin ta tana kuka bayyaso ko kad’an. “Niba wancan ba” ta ce tana kukan still. Sosai taji dad’i daya yaba kyanta haka. “Toh meneh Fannah? Stop crying please” “Anas ba kyau, akace da namiji ya tab’a jikin macen daba muharramarsa ba gomma yatab’a garwashi, azabansa kuwa yafi ad’au k’usa a buga masa a kai har se ya nitse. Anas banason amaka wannan azaba, banaso please kadena rik’e min hannu gomma ace ma muna da aure ne kake rik’emin hannun I wouldn’t mind amman a yanzu haka haramun ne, kadena kaji? Banason amaka wannan azaba, please.” ta k’are maganar tana hawaye. Shiru yayi chan yace a hankali “shine dalilin da kike kuka?” Kai ta giad’a masa a hankali har yanzu bata bar kukan ba. Hannunta ya sake a hankali “toh ya isa daga yau barin sake rik’e miki hannu ba kinji? Stop crying.” Da murmushi a fuskarta ta d’ago kai tana kallonsa “promise?” Kai ya giad’a mata. “Bani kad’ai ba kowace mace baraka sake rik’e mata hannu ba?” Nanma kai ya giad’a, “what of Amal? Har itama?” Ya tambayeta. “Amal muharramar kace zaka iya rik’e mata hannu da ita da Ummie amman banda matan waje.” “Okay...” ya fad’a yana giad’a kai. “Cry nomore kinji? Barin k’ara ba” Tana murmushi ta giad’a masa kai “I won’t ever. Thank you Anas lets go?” “Yes lets go.” Yayi assuring nata, da a dana ne hannunta cikin nasa zasu fice amman banda yanzu. Side-by-side kawai suke tafiyar. Bayan sunfito suka sami Afrah da Shettima zaune kan wata doguwar kujera sun baje se hira suke suna dariya kamar wanda suka jima da sanin junansu. “A ina suka saba?” Anas da Fannah suka tambayi juna a tare. “Nima bansani ba” suka sake amsar junansu a tare. Murmushi kad’an suka saki. “Shettima fa baida matsala ina shi ina Afrah?” ya tambaya cike da mamaki. “No let them be please karka mishi magana.” Cewar Fannah cikin salon da dazaran tama Anas magana dashi yake amincewa da k’udurinta. “Fannah amman kina ganin is okay?” “Yes don’t bother, lets go.” Bayan ta ajiye wa Amal birthday present nata taja hannun Aiman, ai atapir Amal tace se Aiman ta kwana mata, ita a dole tasamu sister. Da k’yar ta amince tabar Aiman ta tafi bayan ta kwashe mata kusan rabin birthday present nata tabata. “Toh Afrah seki tashi ai mutafi ko? Soyayyar ya isa.” cewar Fannah. Murmushin jin dad’i Shettima ya saki a yayinda kunya ya ratsa Afrah musamman ma dataga Ya Anas gefen Ya Fannah yana kallonsu. “A’a kuje ni zan kaita.” Cewar Shettima. Anas zeyi magana Fannah ta dakatar dashi “lets go ze kawo ta yace.” Badan Anas naso ba yabi Fannah suka fice. *kuyi min uzuri please da rashin posting da nakeyi kwana biyu, somethings came up* *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:54, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 5⃣3⃣ Ba Afrah ce ta dawo gidah ba se bayan Maghrib, hankalin Mami duk yabi ya tashi dukda kuwa Fannah ta tabbatar mata cewar Afrah is safe with Shettima k’anin Anas. “Shettima thank you for today.” Cewar Afrah alokacin da take k’ok’arin bud’e murfin motan. “No let me babe” nan ya zagayo ya bud’e mata tare da ciro shopping bags guda biyu daya cika mata da kayaki. “Will call you as soon as na isa gidah, I love you My Afrah.” Tana murmushin jin dad’i tace, “I love you too My Shettima” ahaka suka rabu. Taku take a hankali gudun kar a jiyota aiko tana shiga suka had’u da Aiman kafin tace meh Aiman ta sa ihu “Mami ga Ya Afrah ta dawo.” A 360 Mami da Fannah suka fito. “Ke Afrah zo nan” cewar Mami kai a sunkuye ta k’ariso kafin Mami ta fara mata masifa ta kare kanta ta hanyar yin k’arya “Mami wallahi motarsace ta samu matsala seda muka kira me giara.” “Uhn uhn fa Afrah kiyi a hankali daga had’uwan ki da yaro seku zarce da soyayya?” “La ilahi! Mami abakin wa kikaji wannan zance?” “Ni na fad’a mata ai ba k’arya bane” cewar Aiman. “Mami wallahi har zama sukayi gu d’aya.” “Ai Aiman barta-” “Mami yi hak’uri ya isa zan mata magana” Fannah ta katse ta a hankali cikin dabara. “Afrah mushiga daga ciki.” Amsar d’ayar ledan hannun nata tayi sukayi d’akinsu. Bayan sun baje kan gado Fannah ta soma mata magana; “Afrah ni bawai hanaki zanba amman ki bi komi a hankali kinji? Na miji na miji ne.” “Ya Fannah wai nikan hassada akemin neh? Me aciki keda Ya Anas nida Shettima darling kin-” bata k’are maganar ba wayarta ya soma ruri tana kai dubanta taga Shettima ne datayi saving da ‘hot baby.’ Karap ta d’aga. “Hello baby” tace a nitse cikin wata salon da Fannah bata tab'a saninta dashi ba. Baki ta bud’e cike da mamaki tana kallonta haka har Afrah tagama wayar ta katse Fannah bata bar kallonta ba. “Har haka soyayyar taku tayi nisa?” “Hummn!” Taja numfashi, “Ya Fannah kenan, guguwar son Shettima ne ya kamani, wallahi ya had’un had’ewa duk abinda nake nema jikin d’a na miji yaja dashi. Daman ni dream d’ina na auri kyakkyawa sega Shettima nan Allah ya kawo min.” “Awww! Har tunanin auransa kike?” Cewar Fannah baki wangalau. “Humm! aini barni kurum har yaran da muka haifa ma na hango, barni in duba kayakin da ya sissiyo min ma tukun.” ★★★★★ “Ya Anas in shigo?” Cewar Shettima dake tsaye bakin k’ofar Anas. “Shigo” ya basa amsa. A nitse ya bud’e k’ofar ba kamar yadda ya saba ba, ‘yar vest na Anas dake k’asa ya d’aga “Ya Anas in sa maka wannan cikin laundry basket?” Kallonsa Anas yake yau wata rana. “Eh sa” yabasa amsa. Bayan yasa yadawo ya zauna kusa dashi. “Ya Anas dan Allah alfarma nike nema.” “Name fah?” Cewar Anas yana duban laptop nasa. “Ya Anas bundle na d’ari biyar zaka bani please.” Ajiye laptop d’in yayi gefe guda cike da mamaki, “Shettima yaushe ne na baka na 200 da zakace in baka na 500 yanzu? Me kake da kud’in. Awww! Kaima kasan kayi girlfriend ko? LOL ba abinda zan baka, go and work for it, earn it!” “Ya Anas mana please, wallahi na mayar da hanakalina wajen karatu yanzu ka taimaka please.” “Amman Shettima kai kanada hankali mah kuwa? Ina zaka kai Afrah?” “Ni Ya Anas banche ka zageni ba, kud’i kawai zaka ban.” “Aww kawai ne? Sekayi kashinsa ai tunda kawai ne.” “A’a Ya Anas please yi hak’uri.” “Naji banasan surutu ina ganinka bud’e safe d’in d’au d’aya kabani waje.” Tsalle ya daka yana masa godiya sannan ya zaro d’aya daya lek’a yaga Anas bai kallonsa ya k’ara d’aya tare da b’oyewa cikin kayansa. “Uhm Ya Anas dama nace batun mota ta wallahi ta tsufa tasoma shan mai ko za’a d’an canza min.” Maganar da yayi kad’ai yasa Anas shak’ewa harda tari. Dududu shekarar motar nawa ne? Da k’yar inya kai d’aya shine Shettima ke wannan zance. “Ai da fili kafito kawai kace min kayi budurwa kaima kanasan ka fara hawa babban mota irin nawa.” “A’a wallahi Ya Anas ni ko E350 ka siya min walillahil hamdh Allah zan karb’a, kaji Ya Anas.” “Hehehe! su Shettima an girma har ansan ayi budurwa.” “Ya Anas mana...” “Naji in naga kayi hankali zan canza maka motar, inko a’a zaka cigaba da zama da C 230 d’inka.” “Thank you so much Ya Anas, nagode, Allah bar mana kai ya k’ara dank’on soyayya tsakanin ka da Fannah.” Bejira jin meh Anas zece ba yafice. Murmushi ya saki jin an ambato sunan Fannah, shi yau through out ma besha coffeen ta ba, yayi missing inshi kuwa sosai, wayarsa ya lalimo ya danna mata kira bada dad’ewa ba ta d’aga “hello Anas.” “Fannah” yakira sunanta. “Na’am” ta amsa. “Yau bansha coffee ba.” “Yi hak’uri gobe zanzo in had’a maka.” “Har gobe?” ya tambayeta cikin wani irin salo cike da damuwa. “Toh Anas ai bareyi infito yanzu ba yayi dare, goben kaji?” Shiru yayi bece komai ba. “Kaji Anas?” “Naji” yace chan k’asa k’asa. “Yawwa goodnight” sannan ta katse. Ji yake kamar ya sake kiranta bai gajiya da jin muryarta amman kuma bayyasan ta raina sa ta d’au ko sonta yake. Bayan ya idar da isha yayi forcing kansa yayi bacci da k’yar danko yunwa yakeji kamar hauka. Washegari ya tashi as usual ya soma shirin office yashiga wanka kafin yafito yaga an share masa d’aki anyi mopping an gyara gado, toh waye ne? Yaushe Amal ta share nata d’akin bale ta share masa nasa, ganin baida amsar wannan tambaya kawai yayi shirinsa yana fitowa yaga shock of his life, Shettima har yagama tsara masa breakfast da alama sharan d’akin ma shi yayi. “Shettima?” Anas ya kira sunansa still not believing abinda idanunsa suke gane masa. “Na’am Ya Anas good morning bismillah ga breakfast nan na had’a maka.” A hankali ya tako ya zauna kan kujerar Shettima ya zuba masa chips da scarmbled egg daya masa, sannan ya had’a masa tea. “Tsaya aljanu ne suka shige ka komeh?” Anas ya tambaya. “Aljanu kuma Ya Anas? Dan na had’awa wa Yaya na guda breakfast se ace aljanu sun kamani?” “Toh d’akina fah? Kai ka share?” “Eh Ya Anas bismillah ci kar kayi latti.” A zuci Anas yace ahhh lalle Shettima nasan in canza masa mota LOL gaba ta kaini, nasamu new man servant. Koda yagama breakfast d’in Shettima ne yakai masa jaka mota. Tuk’i yake hankalinsa kwance Baana ya danna masa kira cike da jin dad’i ya d’aga. “Maza ne!!” Yace yana murmushin jin dad’i. “Blue eyes nashigo gari fah jiya.” “Ohh haba! Shine baka fad’amin ba?” “Wallahi tafiyan dare ne, zanzo office naka yau.” “Toh sekazo, Kashim fah?” “Wancan? Ai yana chan a Bama ya washi tafiya.” “Kace be canza ba kenan, anyhow ina jiranka.” Ding! Ya katse wayar. Kamar kullum aka bisa da gaisuwa har zuwa office nasa, bada dad’ewa ba Kacallah yashigo da complain, na barin gidan man engine da akayi a dalilin haka ya b’aci se an kira me gyara. Bayan da ya gama karantawa yace, “fire him, ka kori me aikin ai ganganci ne yasa sa mancewa be rufe gidan man ba, ka kuma yi replacing nasa with someone better, clear?” “Yyy... Yes Sir.” 8:30AM yama Fannah a building, kamar jirarta Sule me kula da engine yake, yana ganinta ya nufo ta dan yaji intama Boss magana yana saurarenta. Bayan ya gaisheta yake bata labarin abinda ya faru, “wallahi Hajiya waya aka min mata ta tana labour kuma ba motan da ze kaita sesa duk na rikice na mance ban rufe gidan man ba, dan Allah kima Boss magana ya dawo min da aiki na, in na rasa aikin nan bansan dameh zan ciyar da matata da d’an mu data haifa ba.” Tausayin sule ne gabad’ai ya ratsa ta. “Don’t worry kaji? Zan masa magana in shaa Allah ze dawo maka da aikinka.” “Godiya nake Hajiya, Allah saka miki da alkhairi.” “Ameen” tace sannan ta fice. Bayan tayi knocking yace, “enter” a nitse ta bud’e k’ofar ta shiga tun daga chan yake kallonta, wata skyblue silky doguwar riga ne a jikinta me dogon hannu, seda kuma red gyale d’an siriri data yafa ta nannad’e a wuyarta. Jaka da takalminta kuwa fari ne. Kallonta yake har yanzu, yafisan ganinta ba hijabi tafi kyau, bayan ta k’ariso gaban table nasa ta gaishesa ba takan gaisuwar yake ba ko amsawa beyi ba “kinyi kyau” yace mata. Tana murmushin jin dad’i tace, “thank you” tare da juyawa nan da nan ta had’a masa coffee, ko ina taje idanunsa na kanta, bayan ta had’a ta kawo masa ta ajiye a gabansa. Ba tare da b’ata lokaci ba ya soma sha tana tsaye a gefensa seda taga ya ajiye cup d’in tace, “Sir.” Kai ya girgiza mata “Anas.” Ya gyarata. “Okay Anas nace ba batun firing Sule da kayi ne dama.” “What about him?” Ya tambaya yana kallonta. “Yabar min gidan mai a bud’e yayi destroying engine d’in sena kira me gyara fa yanzu, he is not paying attention to his work.” “Ayyah Anas ba haka bane, matarsa ce tashiga labour shine aka kirasa hankalinsa ya matuk’ar tashi. Dalilin dayasa ya mance kenan.” “Wancan kuma damuwansa, he is fired and that stays that.” “Anas ka dawo masa da aikinsa please, kaji? For me please.” Shiru yayi be ce komai ba. “Please kaji?” Nanma shiru. Kukan da baya bata wahalan yi ta soma take hankalinsa ya tashi. “Toh kukan me kuma?” Cikin kukan tace, “ka dawo masa da aikinsa please.” “Fannah NO!” Wani sabon kukan ta k’irk’iro harda me sauti. “Fannah for goodness sake me haka kitayin kuka? In na dawo masa da aikin zaki bari?” Kai ta giad’a “okay, okay naji stop crying.” “Se ka kira Adam kace adawo dashi zan dena.” Take yakira Adam, “bring back Sule aikinsa.” Ya katse. “Shikenan zaki bar kukan?” “Eh” tace tare da share hawayenta. “Thank you Anas.” Wajen coffee machine ta nufa dan had’a masa cikin flask. Knock ne yazo daga bakin k’ofa “come in” Anas yace. K’ofar na bud’uwa sega Baana bayan ya k’ariso sukayi manshake se hirar su suke irin tasu ta maza nan da nan Fannah tagama d’ura masa coffeen cikin flask, ko d’aga kai taga wayene batai ba. “Sir nagama zan tafi” kafin ya amsata ta fice. “Woooww!” Baana yayi exclaiming. “Maza wannan me zubin india fah?” “Kai de halinka na son mata na nan har yanzu ko?” “Me za’a fasa? Gaskia tamin inaso.” “Kanaso?” Anas ya tambaya tare da d’age gira. Kai Baana ya giad’a masa yana assuring nasa. “Lallai kam tun wuri ma gomma ka hak’ura wannan tafi k’arfin ka.” “Ban tsammanin akoi macen da zata fi k’arfi na yanzu, sufa mata kud’i kawai suke bi wallahi yau da za’ace biri goggo yazama billonaire mata zasu bisa su auresa, so ya za’ayi ne in samu lambarta?” “You are wrong Baana, kaga wannan duniya da abinda ke cikinta be dameta ba, your money will never impress her, she is different from all other women, saboda haka ka fita daga harkanta.” “Kode kaima kana ciki ne?” “Ai itace matar da zan aura.” “Aure Anas!” Ya tambaya yana zaro ido. “Yaushe a gari?” “Nide na fad’a maka kafita kabar harkan Fannah wallahi dan akanta se mu b’ata.” “Allahu Akbar! Maza kaine kuwa? What changed you haka?” “Fannah, she is the one who changed me.” ★★★★★ *MOROCCO, 2:15PM* _Cikin_ _*Royal Mansour Marrakech Hotel.*_ Kwance Anas yke bisa kaftareren California bed ya d’aga pillow tare da jingina ajiki, da isarsu Morocco shida Kacallah awa biyu kenan yanzu. Jiran sim card daya aiki Kacallah siyo masa yake, through out yau be sha coffeen Fannah ba, besata a ido ba, bekuma ji muryarta ba, seji yake kamar ya rasa wani sassa a jikinsa Kafin subar Nigeria yaso kiranta amman girman kai ya hanasa sekuma yanzu yake regreting. Bada d’adewa ba Kacallah ya kawo masa yana sa sim d’in ko gida be kira ba ya zuba number’n Fannah. **** Tana kishingid’e a kan gado ita d’ayanta tana buga game a wayarta ya soma ruri ganin international number yasa bata d’aga da wuri ba. A hankali ta sa a kunne “hello.” “Fannah” ya kira sunanta. “Na’am Anas, ina wuni?” “Lafiya” ya amsa blankly. “Uhm har kun isa ne?” “Eh you didn’t even mind calling me.” “I’m sorry, so yaushe zaka dawo?” “Are you missing me already?” Ya tambaya yana jin dad’i. “Yes I am missing you, I’m missing your your girman kai da masifa.” “Ai nabar yin masifa yanzu.” “Anya kuwa?” Ta tambaya tana murmushi. “Yes, nikuma I’m missing your coffee, your crying and face.” Dad’i sosai taji ya ratsa ta, wannan na d’aya daga cikin abubuwan da takeson Anas, he is very sincere komin ya gaskia take yana fad’i unlike ita, itama tayi missing kyakkyawar fuskarsa sabida rabuwansu da juna tin ran tuesday yau thursday amman ta b’oye masa. “To be sincere I miss your face you too.” “I know you would, dole zakiyi missing handsome face d’ina ga kuma unguwan ku ba kyawawa ko?” “Mr. Fauzi kaga irin halinkan ba, sesa banasan fad’a maka abu kacika feeling dayawa, I have to go Mami na kira na.” Karap ta katse tana murmushi, bawani Mamin dake kirarta bata san me zata ce masa bane kawai, duk lokacin da take waya dashi setanajin wani iri. Shigowar Afrah d’akin kenan ansha gayu kamar ba gobe, “Afrah ina zuwa haka?” “Wallahi hot baby na ne yazo, yana jira na ma yanzu haka. Madubi nazo kalla in fice” aiko tana ganin kanta ta fice. Tsaye tasame Shettima yayi crossing arms da legs jikin motarsa sanye yake da wata farar half jampa. “My queen kinyi kyau” yace da ita alokacin data gama k’arisowa kusa dashi. “You too my king.” Hira suka sha kamar ba gobe se kusan Maghrib yace ze tafi bundle na d’ari biyar ya tsakulo a aljihunsa ya bata. Ido tazaro “hot baby duka wannan?” “Eh nakine sweetie, jiya mun samu profit sosai a business namu shine nima nace barin kawo miki rabon ki.” “Thank you hot baby” ta amsa. Bayan ta dawo ciki ta wula kan gado ta sami Fannah. “Ya Fannah you won’t believe this.” Bandir na d’ari biyar d’in ta ciro ta miqa mata. “Ke ina kika samo wannan?” “Hot baby na yabani.” “Shettiman? Aina yasamu? Yana aiki ne?” “Yana business mana.” “Business? Toh aini bansani ba. Ke Afrah bafa haka ake soyayya ba, ai kika cigaba da amsar kud’i dayawa haka gunsa seki talautar dashi.” “Toh ai bani yayi ba rok’a nayi ba. Wayyo! A gobe zanje in siyo Iphone nima.” **** Chan dare misalin k’arfe goma sha d’ayan dare a Morocco ko bacci Anas yakasa se juye-juye yake, ga gajiya amman yakasa baccin ba abinda yake inbanda tunanin Fannah. “Oh God! What is wrong with me? Why can’t I think of anyone se Fannah? Why?” Pillow ya d’au ya rufe fuskarsa dashi ko ze d’an rage tunaninta, ai se worse ma yake. Wayarsa ya d’ago daga kan bed side drawer ya kirata. Tana cikin baccinta tajiyo ringing na wayarta kamar wacce zatayi kuka ta d’aga ko duba wanda ke kira batai ba. “Fannah” ya kira sunanta. Jin muryarsa ta tashi ta zauna. “Mr. Fauzi what is it?” Ta tambaya cikin bacci. “What are you doing?” “Bacci mana” ta amsa sa a takaice rai ad’an b’ace. “Okay shikenan” ya fad’a kamar d’an yaron da aka mai rowan sweet ya katse wayar. Wayar ta ajiye ta koma bacci sede kuma daga yadda Anas ya mata maganar kamar bacci ya kasa, sekuma taji tausayinsa yaje chan besan kowa ba wayar nata taja ta kirasa yana gani yak’i d’agawa. “Toh ko har yayi bacci ne? Barin sake gwadawa inga.” A karo na biyu ne ya d’aga “Anas” ta kira sunansa a hankali, jin shiru tace. “Anas are you there?” “Yes” yace chan k’asa k’asa. “Ka kasa bacci ne?” Nama “yes” yace. Shiru tayi tana nazarin me zata ce masa chan tace, “uhm if you need someone to talk to I’m here for you.” “Just go, jeki kwanta.” “Anas kaifa?” “I can’t sleep” yanason yace mata saboda yana missing nata ne ya kasa bacci amman kuma yak’i. “I can’t either.” Ta fad’a. “Why? Ba bacci kikeyi ba yanzu?” “Not anymore, you can’t sleep I’ll stay awake with you.” Dad’i yaji sosai. “Are you sure?” “Yes” ta fad’a tana giad’a kai. “Thank you.” “So yaushe zaka dawo?” “Maybe in 3-4 days time.” “Okay Allah kaimu.” “Ameen, so ya Afrah da Shettima?” “D’azu ma yazo wajenta, wai dama Shettima na business?” “Business kuma wani erin business kenan?” Anas ya tamabaya cike da rashin fahimta. “Nima I don’t know haka yace mata wai yana business harda kawo mata bundle na N500 dayazo.” “Are you serious?? Lallai ma Shettima, abinda zeyi da kud’in kenan dama. LOL” “Kamar ya Anas?” Nan ya labarta mata yadda Shettima yasamu kud’in. Dariya sosai dukansu suka b’arke da. Haka sukata hira kamar ba gobe sekace ba Mr. Fauzi ba, sun fi awa suna waya har bacci ya sace Fannah. Jin shiru ya kira sunanta, shiru bata amsa ba “kinyi bacci ne?” Nanma shiru. “Goodnight” ya fad’a ahankali, k’in kashe wayar yayi yana d’an jin nishin Fannah da haka shima ya samu yayi bacci wayar mak’ale a kunnesa. *©miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:54, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 5⃣5⃣ Shirye shiryen biki aka soma da zafi-zafi ba makawa, koda Anas ya sanar da Abuu be gama gina gidansa ba shida Fannah zasu zauna a hotel for the mean time bayan bikin ba’a samu matsala ba, Abuu ya amiche haka zalika su Baba ma. Duk wani had’in magunan addini na gyaran jiki Mami ta tanadar wa Fannah, itade Fannah ba wanda take sha saboda ba point koda ta sha. Tun ranan da aka yo tambaya aka sa rana, kalma be sake had’a Anas da Fannah ba, iya k’ok’arinsa yake ya mance da ita tun batun da Baana yataho masa dashi. Akan ya kuskura yacigaba da coming in contact da Fannah to dole soyayyan dayake k’ok’arin kashewa yayi rising yazamo end nasa kenan. Shikuma abinda bayya so kenan, bayason soyayyar dayake ma Fannah yaje ko ina dan haka yafita daga harkarta gabad’aya. Ta fannin Fannah ma dad’i taji atleast kwana biyu da bayya kirarta tsoron da take masan ma ya d’an ragu. Ko Shettima besan contract marriage ne tsakanin Anas da Fannah ba. Inbanda Baana ba wanda yasani, shima d’in dan ya fiye gane-gane ne Anas ya sanar dashi. Ana saura sati uku biki ne su Ummie suka kawo kayan lefe, komi ita ta siya kud’i kawai Anas ya bada. Akwatuna ne turum ba adadi, koban fad’a ba kuma kunsan ya auren youngest billonaire ze kasance komai over aka yisa. Kud’in d’inkin da aka kawo ma nan yayi over. Abinda ya kama gowns da Fannah zata sa a duk events da za’ayi sun d’inka sun kai mata. Ummie che tasa Anas a gaba se anyi events d’in dan ko kad’an baya so, shi be k’i a tofe fatiha ba kad’ai. ★★★★ A yau ana sauran sati biki, tsabagen tunani har wani rama Fannah tayi. Zaune take ta had’a tagumi a d’aki da plate na abincinta gabanta da alama ko tab’awa batayi ba, da shigowar Mami kusan minti biyu ammmana Fannah batayi noticing inta ba tsabagen yadda tayi zurfi cikin tunani. “Habibti” Mami ta kira ta cikin salon mahaifiya cike tausayi. A firgice ta d’ago kai “na’am Mami, yaushe kika shigo?” Bayan Mami ta zauna a kusa da ita tace, “Habibti wai me haka ne? Tun da aka sa ranar bikin nan kika soya, tunanin me kike?” “Mami babu” ta mata k’arya. “Ko bakison Anas d’inne naga ko duban kayan lefen bakiyi ba.” “Ina sonsa mana Mami.” tayi faking murmushi. “Toh magunanki fa kina sha? Kinsha yau fa safe?” “Eh Mami nasha.” “Ki gama cin abincin ki, seki huta zuwa anjima me gyaran jikin zatazo kema kin sani.” “Mami ni walllahi asaran kud’i ne kawai wannan abu, na fad’a miki ba amfani.” “Yoh! Ji ‘yar mutane. Ummie su kawo kud’i suce ayi maki gyaran jiki sekice asaran kud’i? Uhn uhn fa Fannah, tam! Maza gama ci ki huta.” Tana kaiwa nan ta fice. ***** “Ummie wai dan Allah se anyi wani shirmen dinner d’innan ne?” Cewar Anas daya baje kan gado da wayarsa a hannu se latsawa yake. “Se anyi Anas ace bikin d’a na guda bikin billonaire kamar ka bara ayi hidima ba? Ni na fad’a maka kayi kayi ka amso d’inkunan ka gun tailor nan. Nan da gobe za’a fara events d’in.” Banza yayi da ita. “Ko bakaji ba?” “Naji” yabata amsa blankly. Bayan ta fita ya saki numfashi tare da rufe idanunsa yana tunanin wai aure zeyi in just a week time. Kap friends nasa ba wanda ya yarda dayayi inviting nasu d’aurin auren, suna ganin invitation card amman sunka k’i yarda. Ya rasa me ke damunsa yanzu, a da daya tafi Morocco tsantsan yadda yake missing Fannah yasa yayi pushing through da maganan auren amman a yanzu seyaji bayaso, dukda kuwa contract marriage ne amman bayyaso anymore, yasani the more suke cigaba da zama under thesame roof da Fannah he will develop feelings for her sesa ya yanke hukunci koda anyi bikin bare na shiga harkarta ba bayan wata shida ya sallameta ta huta shima ya huta. Rurin da wayar sa ya soma yi ne ya tsamo sa daga duniyar tunanin daya wula. ‘Fannah’ yaga rubuce kan screen d’in. Yana gani har call d’in ta tsinke be d’aga ba se a karo na biyu nan ma be amsa ba. “Hello Mr. Fauzi” siririyar muryata tace. “Yes Miss Aleeyu” ya amsa back. Sosai yayi missing muryarta, fuskarta and everything amman babu kamar coffeen ta. “Mr. Fauzi batun wedding events d’inne nace please kasa ayi cancelling.” “Why?” Ya tambayeta straight forward kafin ta amsa yace, “nid’in an fad’i miki so nake ne? Auren entirely ma ba so nake ba, so kamar yadda nayi hak’uri kema yazamo miki dole kiyi hak’uri ayi komi ya k’are. Is this the reason why you called?” Chan k’asa k’asa tace, “yes.” “Then I’m hanging up.” Karap ya katse wayar. Takaici ne da bak’in ciki ya rufe Fannah. Wai mesa Mr. Fauzi yake behaving haka? Ko wani abun ta masa? Inma hakan ne chan ta matse masa. _1 day later..._ A yau ne aka soma events na bikin ANAS IBRAHIM FAUZI dakuma FANNAH ALEEYU. Da walimah aka soma wanda Anas beje ba. Kyau kam ban tab’a gabin Fannah tayi erinsa kamar na yau ba, danko this is her first time applying heavy makeup. Sede sam ba fara’a a fuskarta kasancewar aske mata gira da makeup artist tata tamata wanda batasan tayi ba seda aka gama. Sosai taji haushi tata mata masifa kuma. Tsayuwa dan bayanin had’uwan wajen kuma b’ata lokaci ne, wajen cike yake da fans na (Tana Tare Da Ni) kowani corner na wajen su ne duk sunsha kyau cikin bak’in aboyoyinsu. Wa’azi sosai aka zage wajen wanda har yasa Fannah kuka in ta tuna ba auren gaske bane. The next day akayi English dinner wanda Anas yasha b’akar suit nasa da white shirt ta ciki dakuma black tie, kyau kam mashaa Allah a yayinda Fannah take sake da white ball gown. Duk sunyi kyau. Fans de su suka cike hall d’in kowacce tasha had’ad’d’en gown nata se kashe selfie akeyi da Mr. Fauzi kad’an ne masuyi da Fannah sabida duk masu son Mr. Fauzi ne cike wajen nima de ina d’aya daga cikinsu. The next day akayi Mother’s Eve wanda Anas yasha farar babbar rigar da ban tab’a ganinsa ciki ba. Tsayuwa dan bayanin kyan da yayi shima b’ata lokaci ne. Kamar yadda yayi kyau haka ma Fannah tayi. Makeup artist nata gaba take wajen fidda kyan mutum. Itama farar gown ne a jikinta. Shikansa Anas yakasa d’auke idanunsa daga kan Fannah, skin nata wani glowing yake dan yadda yasha gyara. 2 more days aka d’auka ana events, a takaice events biyar akayi a bikin wanda a safiyar ranar Asabar aka d’aura auren ANAS IBRAHIM FAUZI da FANNAH ALEEYU akan sadaki dubu d’ari biyu da gwalagwale. Da yammacin ranan su Ummie da sauran dangin miji sukazo d’aukan amaryarsu. Kukan da Fannah tayi bana misantuwa bane har cewa take ta fasa auren ma ita kawai Anas ya saketa. Kuka take wanda har tasa Mami dasu Afrah ma, Aiman kam sanda tama wata babbar mace rashin kunya ita sam a bar mata Ya Fannar ta. Da hawaye da majina aka samu aka ciro Fannah daga gidansu. Kwalyan yau shine beyi kyau ba cikin sauran dan yadda fuskar nata ya kumbura tam idanun sunyi ja suma sun kumbura. Shikansa Anas daya ga fuskarta a wajen event d’in seda yaji wani eri, wani irin kuka tayi? Wani irin hawaye tayi asararsu a yau? How he wished he was there da take kukan ya hanata. Daga wajen dinner driver ya wuce da Fannah da Anas masauk’insu. Ba abinda take cikin motar se kuka ba makawa afarko yayi niyyan ya share ta dan ma wani haushi ta soma basa, sekace aljani aka aura mata ai yaga shima ba san auren yake ba inji sa da fad’i. Shi mesa bai kukan se ita? Ganin tak’i yin shiru yace; “Fannah kukan ya isa mana, meh hakan please? Ke kikayi signing da kanki to kukan meh?” “Ni na fasa, nafasa kawai ka kaini gidanmu dan Allah.” “Aww hakane? Toh nak’i bara a kaikin ba, ai ke kikayi signing da kanki. Driver lets go I beg.” Sautin kukanta ta k’ara ayayinda ya ciro headphone ya k’ure da wak’a a farko, sekuma ya tuna wa’azin da Fannah ta masa dukda ayanzu haushi take basa seyaji still bayason ya sab’a wa promise daya d’aukar mata. Switching yayi daga wak’a ya miyar qira’a sautin Sudais. Haka ta ta kuka har seda suka iso hotel d’in. Tafito ma tak’i. “Fannah wai me haka ne? I’m tired I want to rest kifito lets go will you?” Ko tanka sa batayi ba se kukan ta data tasananta. “Ohhhh God!” ya fad’i a fusace. Zagayo wa yayi ya bud’o k’ofar natan tare da finciko ta da hannu. Se k’ok’arin k’watan hannunta take amman takasa be saurara mata ba seda suka isa har d’akinsu bayan ya rufe k’ofar ya sake ta. K’asa ta sauk’a tana kuka. “Thank God na fito da headphone d’ina.” yace tare da mak’ala headphone d’in a kunnensa ya zauna kan wata couch tare da juya mata baya. Bare iya sauraron kukanta ba kamar yadda bare iya ce mata tayi hak’uri ba saboda haushin data basa na kukan da take tayi. Tafi minti talatin tana kuka wajen, ganin ba ubangiji se Allah ta tashi tare da tattara gown nata, inda aka ajiye mata kad’an daga cikin akwatinta ta nufa tare da jawo na kayan baccin ta. Toilet ta nufa dashi se anan Anas ya juyo yaga tarufe k’ofar toilet d’in. Rigar jikinsa ya rage ya bar daga vest se short nicker. Wayarsa ya d’auko yana d’an danne-dannensa ciki chan ya kira waya ya musu ordering abinci dan rabuwansa da abinci tun breakfast he is sure Fannah ma haka. Fried rice and chicken lafiyayye aka kawo musu plates biyu, ko tab’a wa beyi ba yana jiran fitowarta su ci tare. Doguwar tuska Fannah taja a bathroom d’in wanda daba dan famfo na a bud’e ba da Anas ya jiyo ta. Akwatin tas ta zazzage ba kayan baccin daya mata duk sunyi tsireci dayawa daga wanda sama a bud’e se wanda k’asa a bud’e se wanda tsayin dududu iya guiwa ne. Kamar wacce zata sakeyin kuka ta soma miyar dasu cikin akwatin duk takaici yabi ya isheta. Chan tasamu wani d’an dama dama ciki tsayinsa iya guiwa ne yanada dogon hannu amman kuma transparent. Wajen k’irjinta kuwa kad’an ne a bud’e, ahakan wai shine salihi cikin night gowns d’in. Bayan ta ajiyesa a gefe ta soma jan zip nata dan cire babban gown me uban nauyin dayake jikin nata. Dambe take da zip d’in amman takasa ja, harda guntun hawayenta. Ganin ba ubangiji se Allah ta ciro wayarta daga jakar ta dannawa Mami kira tana kuka sama sama. “Hello Habibti na.” “Mami” takira sunanta cikin sautin kuka. “Habibti kukan be isa bane har yanzu?” “Mami dan Allah kizo ki d’aukeni mu koma gida dan Allah.” “Wace erin magana kike Fannah? A fasa auren kenan ko meh?” “Eh Mami a fasa na hak’ura.” “Fannah ai hak’uri zakiyi nima haka na hak’ura, nan da lokaci k’alilan zaki saba kinji Habibti?” “Mami tsoro nakeji.” “Ya isa haka kinji? Ba abinda ze faru in shaa Allah.” Majina taja, “Mami na kasa jan zip d’ina kizo ki ja min please.” “Habibti yaushe ne zan bar gida inzo har inda kike na ja miki zip d’in? Ina Anas yake?” “Mami ni bansani ba dan Allah kizo.” “Kiga Fannah jeki sami Anas kice ya ja miki zip d’in kinji? Ze ja miki.” Kuka ta fashe da cikin wayar. “Mami ni banaso dan Allah kizo.” Da k’yar Mami tayi convincing nata ta yarda zataje tasamu Anas d’in. Bayan ta ajiye wayar ta wanke fuskarta data kumburo kamar ba gobe. Anas bawan Allah har yagaji da jirarta amman still be tab’a abincin ba. K’in fitowa daga bathroom d’in tayi se k’ok’arin jan zip d’in take ganin ba mahalicci se Allah ta fito daga baya, kallonta Anas yake danko ya rasa me take tun d’azu ciki. Ba wanka tayi ba, ba kuma rage kayan jikinta tayi ba. Toh me ta tsaya yi? Kallonta yake a yayinda take takowa har gabansa ta k’ariso da kanta a sunkuye ko kallon sa batai ba. A nitse ta juya bayanta tare da tsugunawa, kallonta yake cike da mamaki me take shirin yi? “Sir help me kaja min zip please.” Se yanzu ya gano dalilin daya sa ta jima a bathroom d’in. Yi yayi kamar be jita ba. “Sir please help me” ta fad’a cikin sautin kuka. “I’m not Sir I’m your husband Fannah, so correct yourself.” “Anas kaja min zip d’in please” ta fad’a ba gardama. Zip d’in ya k’are ma kallo sannan ya aza hannunsa akan bayan ta. Wani electrification sukajiyo within them dukansu biyu, kansa ya kawar dan bai son kallon bayan nata gudun abinda ze iya haifar wa. A hankali yaja mata zip d’in zuwa tsakiyar bayanta. Da sauri ta mik’e kafin ya gane mata tsireci. “Thank you” tafad’a a hankali alokacin da ta d’ago kai tana kallonsa. Da mamaki taga bama kallonta yake ba nufin bema ga bayan nata ba keman, hamdala ta saki ganin baida niyan amsa godiyar da ta masa ta koma bayin ta sa lock sannan ta cire kayan, ruwa ta watsa ta goge jikin ta da kayan data ciren sannan tasa na baccin. Babban hijabin ta data d’inka na musamman ta zira akai tafito tare da jawo akwatin nata. Ko kad’an Anas be kallanta. Akwatin ta miyar inda ta d‘aukosa. “Come lets eat” yace da ita. “I’m not hungry.” “Fannah banason surutu, you didn’t eat I know kizo muci abinci.” “Banajin yunwa.” ta fad’a dukda kuwa yunwa takeji kamar ba gobe, rabuwarta da abinci tun safiya sede batada appetite na cin abincin ma. “As your husband nace kizo muci abinci.” Zata sake magana ya daka mata tsawa “now!” A hankali ta tako zuwa inda abincin yake ta d’au plate nakusa da itan daidai zata juya ta koma kan gadon kenan ya rik’e hijabinta “sit here lets eat.” “Anas zanci achan.” “Nikuma mijinki nace anan nakeso.” Gudun tsinuwan mala’ikun rahma ne kad’ai ya sata zama a kusa dashi. Spoons bekai goma ba tayi tace masa ta k’oshi ko tab’a kajin kai batayi ba. Bece mata komai ba illa binta da kallo da yake, wayanta ta duba taga k’arfe 11:30PM. Pillows da aka jera kan gadon wanda sun kusan kai goma ta zubar duka k’asa kallonta Anas yake bece ko uffan ba. “Anas wani side kafiso? Zan kwanta.” Banza yayi da ita. “Kaji Anas?” “I prefer the rightside.” yace cike da nuna rashin damuwa. Tokari taji a zuciyarta wanda harta fuskarta seda ta nuna. Ko a gida a gefen dama take kwanciya, shi Anas kuwa da gangan ya ce gefen daman yafiso dan yasan sarai itama daman zatace tafiso tunda take tsaye ta wajen. Ba dan tanaso ba ta koma leftside d’in tare da tattaro duka pillows d’in shide Anas kallonta yake. One by one tasoma jera pillows d’in ta hanyan yin katanga tsakaninta dashi. Lallai ma Anas yace a zuciyarsa. Me take nufi? Tunani take waiko insun kwanta ze mata wani abu? Toh she is decieving herself. Bece da ita komai ba seda ta gama raba tsakaninsu sannan yace, “ni barin had’a kwanciya dake ba, zan kwanta kan kujerar nan so ki kwantar da hankalinki” ya nuna dogon 3 seater dayake zaune akai. Bata ko kallesa ba sede ta kasa b’oye dad’in da taji. Da hijabinta ta kwanta, bayan tagama tofe addu’o’inta ta rufe ido. Nanne Anas ya tashi ya fad’a bathroom ya watsa ruwa shima. Sabuwar nicker yaciro yasa. D’aya daga cikin blankets dake kan gadon ya zaro da pillow d’aya ya koma kan kushion d’in. Alokacin Fannah tayi nisa da yin bacci, wuta ya kashe ya koma ya kwanta. Da misalin k’arfe 3:23AM na dare Fannah ta farka tare da tsala wani irin ihun daya firgita Anas lokaci guda a sanadin mafarkin data sabayi datayi. “Wayyoo Allah! Dan Allah kayi hak’uri karka tab’ani dan Allah bawan Allah dan Allah.” Hawaye take sosai tana b’ari gawani gumin dake k’eto mata duk da AC’n dake huruwa. “Mami! Mami! Mutumin.” Anas besan lokacin daya taso ya nufo inda take ba. “Fannah wani mutumi kuma?” wani ihun ta sake tsalawa ganin Anas. “Mami wallahi gashi nan ze k’ara, dan Allah kayi hak’uri.” Hankalin Anas ya mugun tashi ganin yadda take kuka fiye da na d’azu duk ta tsorata se b’ari take, murya cike da damuwa yace, “Fannah is me, Anas your husband bawani mutumi.” Ganin yadda take zufa yagano mafarki tayi dan shima anytime yayi mafarki haka yakeyi. “Bar kuka kinji?” Hannunta ya gwada rik’ewa wani irin rikicaccen ihun ta sake saki tare da matsawa baya. Hab’arta ta had’a da guiwa se kuka take tana b’ari... *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com *Kuyi hak’uri da rashin posting da nike two days, wallahi harkoki suka mani yawa, I love you all* [12:54, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 5⃣6⃣ Wani irin tausayin daya jima be mata irinsa ba ya soma jimata yau, azabarcaccen kuka take na hak’ik’a daga ya gwada tab’a koda hannunta ne sekuma ta tsala ihu tana had’asa da Allah. Toh wannan wace erin mafarki ne? Ya tambayi kansa. Kasancewar akoi d’an haske d’akin be damu ya kunna wuta ba, wajen dispenser ya nufa ya tsiyayo mata ruwa a cup cike da tashin hankali. “Fannah gashi sha kinji?” Ko kallonsa batai ba se b’ari da take tana hawaye, “Fannah mafarki ne bawani mutumi anan kinji? Sha ruwan ki koma bacci.” Hannunsa daya aza kan bayan ta taja jikin nata baya da wuri. “Dan Allah kayi hak’uri Mami please kizo wallahi gashi nan.” Cup d’in ya ajiye bisa side drawer tare da finciko ta da hannu seda ta fad’a a jikinsa, gagam ya matse ta a jikinsa me k’amshin bala’i dakuma d’umi, ta hanyan hugging nata. Ihu ta saki sosai tana b’ari a yayinda kukanta ya tsananta sekuma had’a sa da Allah da take tana k’ok’arin k’watan kanta amman sam ta kasa. “Dan Allah kayi hak’uri ka sakeni, kar ka k’ara dan Allah...” “Shhh! Fannah is okay, stop crying kinji? Bawani mutum anan Anas ne kawai, stop fighting it keep calm, I’m here for you bar kuka kinji?” Anas ya sanar da ita cikin wani irin salon da be tab’a using ba, hab’ansa na akan kanta. A hankali ta dena fad’an da takeyi na k’watan kantan sede kukan da take har yanzu bata bari ba. “Is okay kinji? Mafarki ne, I’m here, bar kukan.” Hijabin ta daya jik’e jak’af da gumi yayi yunk’urin cire mata wata ihun tasake tsalawa. “Fannah ba abinda zan miki you are sweating, duk kin jik’e tsaya in cire miki hijabin kinji?” “No banaso dan Allah kayi hak’uri, karka k’ara.” “Ba abinda zan k’ara kawai cire miki zanyi, you’re sweating.” Sam tak’i yarda yacire mata shiko ya dage seya cire saboda irin zufan datake ta had’awa duk wuyan hijabin nata ya jik’e. Da k’ak’ani k’ak’a yasamu ya cire mata hijabin tana manne a jikinsa har yanzu. Sunyi kusan minti goma a haka se daddad’un kalamu yake fad’a mata yana shafa bayanta a hankali, hankalinta yana kwanciya, nan ne tasamu tabar kukan sede numfashinta be dawo saiti ba har yanzu. Bacci sosai Anas yakeji, “Fannah” ya kira sunanta a nitse. Cike da tsoro ta amsa kanta manne a k’irjinsa. “Uhmm” tace. “Ba wani mutumi mafarki ne ba?” Ya tambayeta. Kai ta giad’a a hankali. “Good toh lets go back to sleep, nasan kema kinajin bacci.” Hannunsa daya zagaya a bayanta ya zaro wani tsoro taji ya sake ratsa ta atake batasan lokacin da ta zagaya hannayenta bibbiyu a jikinsa ba gagam ta matsesa not letting go. Wani erin sparks Anas yajiyo within him. “Dan Allah kar ka tafi wallahi mutumin ze dawo.” “Fannah I’m here bare dawo ba, ba tafiya zan ba kinga ina chan, ba mutumin da zezo kinji?” Kai ta girgiza “please kar ka tafi wallahi zezo.” “Fannah we need to sleep, bacci nakeji.” “Anas please...” Ta rok’esa cikin sautin kuka. “Okay okay naji barin tafi ba amman lets sleep kinji? Barin d’auko pillow na se mu kwanta.” Nanma kai ta girgiza da k’yar ta sakesa ya d’auko pillow ahakan ma binsa take hannunta nannad’e cikin nasa. Bayan ya ajiye pillow’nsa kan gadon yace, “oya hau ki kwanta.” “Ina jin tsoro.” “Fannah I’m here.” Ture pillows datayi katanga dasu a jiya yayi a k’asa sannan ya kwanta tana tsaye a kansa se b’ari take. Hannunsa ya bud’e mata “come here.” Ba musu bale gardama ta haura kan gadon itama, hannunta yaja a hankali ta fad’a kan k’irjinsa, kanta ta daidata ta kwanta comfortably a jikinsa, da rabin jikinta akan nasa se b’arin take har yanzu. A nitse ya zagaya hannunsa a bayanta yana shafawa a hankali. “Yi bacci kinji ba mutumin daze zo.” Kai ta gyad’a a hankali tare da yab’a hannunta kan cikinsa ta zagayesa gagam. Ganin bata bar had’a gumi ba har yanzu ya d’an k’ara k’arfin AC’n. A hankali bacci me uban nauyi yayi gaba da Fannah, jin nauyinta a jikinsa ya k’aru ya tabbata tayi bacci. Cike da dabara ya gwada mai da ita wajen kwanciyarta sede anytime ya gwada motsi seta sake matsesa a jikinta. Sau biyu ya gwada janta daga jikinsa amman tak’i sakesa agarin haka ya since mata ribbon. Uban gashinta ya bayyano kamar wadda zeyi kuka ya gwada packing mata gashin amman ya kasa gashi anytime ya gwada janta daga jikinsa seta sake matsesa. Ahaka shima wahalellen bacci yayi gaba dashi da gashin Fannah duk yabi ya cika masa fuska. Asuban fari Fannah ta tashi a hankali ta soma bud’e idanunta har ta bud’e duka ganinta tayi kwance jikin na miji da hannunta zagaye kan cikinsa ihu tayi niyan sakarwa sewani abu ya dakatar da ita. Hannun nata taja daga kan cikinsa da wuri tana d’ago kanta taga Anas ne, meh hakan? Meya kawosa kan gadon? Me takeyi a jikinsa? Bata gama nemo amsoshin tambayoyin nan ba ta tab’a jikinta taji ba hijabinta me zata gani? Gashinta baje a fuskarta da jikinta gabad’aya. Ihun da tayi niyan yi d’azu ta bud’e baki zatayi yanzu, chak tunanin mafarkin da tayi ya fad’o mata akai ya dakatar da ita. Se a yanzu take tuna duk wani abinda ya faru a daren. Kunya taji sosai inta tuna Anas ya ganta da ‘yar kayan dake jikinta dakuma yadda ta riga matsesa a jikinta jiya. Ribbon nata ta lalimo a garin haka ta farkar da Anas tun idanun nasa suna kafewa har ya bud’e su gabad’aya. Idanunsu na had’uwa tayi saurin kawar da kanta bedsheet ta soma ja tana kare k’irjinta. K’aramar tsuka yaja tare da juya mata baya dan cigaba da baccinsa. Ribbon natan take k’ok’arin miyarwa amman takasa batada ma k’arfin kamawa batasan lokacin da tasaki wani wahalallen k’ara ba take Anas ya juyo yakusan minti yana kallonta tayi nan tayi chan amman takasa kama gashin ya tashi ya zauna. Hannu ya mik’a mata da nufin bani. Itako sam bata gane meyake nufi ba. Hannu kawai yasa ya amshi ribbon d’in daga hannunta cike da tsoro ta gwada matsawa baya ayayinda yajawota ta fad’a jikinsa. Uban gashin nata ya soma packing nasu gu d’aya a yayinda take k’ok’arin fisgo jikinta. “Stop it Fannah” yayi warning nata. Ba tare da b’ata lokaci ba ya kama mata gashin a daidai tsakiyar kanta yabar jelan na yawo. Bayan ta d’ago daga jikinsa ta tuttusa jelar ta nannad’e waje d’aya. “Thank you” ta fad’a masa kanta sunkuye. Bece mata komai ba illa observing nata da yake, nan ya gane hijabinta take nema hannu ya mik’a ya d’ago a k’asa tare da mik’a mata. Hannu tasa ta amsa da wuri ta miyar jikinta sannan ta mik’e tashiga bayi, bayan tafito tayi kan Anas taga har ya koma bacci. “Anas” takira sunansa a hankali. Idanunsa kawai ya bud’e be amsa taba. “Asuba tayi ka tashi kayi muyi Sallah.” Bayan daya gama sauraronta seya sake rufe idanun nasa ba tare da ya amsata ba. “Anas kaji?” Ta fad’i. “Naaji!” Ya fad’a a d’an fusace. Mik’ewa yayi daga kan gadon daga shi se nickers nasa, k’are wa jikinsa kallo tayi nan ‘yan seconds sannan tayi saurin kawar da kanta. Ko ta kanta beyi ba ya nufa bathroom kafin yafito ta shimfid’a musu dadduma tana zaman jirar fitowarsa. Bayan ya fito ya zaro wata milk jallabiyansa sabo pil ya zira sannan ya nufa inda tayi musu shimfid’an, ganin ze fara sallan ba ita takira sunansa. “Anas.” “Meh?” Ya amsata a fusace. “Ba tare zamuyi sallan ba?” “Kowa yayi nasa” ya amsa ta a takaice. “Anas but Sallar jam’i yafi lada.” “Da a gida keda su wa kikeyi?” “Dasu Afrah.” “Naji lets pray then.” “Uhm amman se munyi Rakatainul~fajir ba?” Ta sanar dashi kanta a sunkuye. Raka... Rakatainul~fajir? ya nanata a zuciyarsa. “Me kuma rakatainul~fajir?” Ya tambayeta a fili. “Raka’a biyun da akeyi gabanin k’etowar al~fijr.” “Ohhh! Fannah!” Ya fad’a rai ad’an bace tare da sa hannu cikin gashinsa yana hargitsawa. “Ke komai ne sekin had’a masa concussion? Sallan Asuba ma se anyi rakatainul~fajir ne ko meh?” “Anas hadisi ne fa ingancecce, yin nafilar yafi duniya da kanta dakuma duk wani abinda ke cikinta” “Toh naji raka’a nawa ne?” “Biyu ne kacal, a first raka’ah suratul~kafirun na biyu kuma ikhlas.” Kai kawai ya giad’a mata yajasu. Ita Fannah bata zata ma Anas ya iya Sallah kamar yadda yajasu ba, ta d’au ko sallan ma seta koya masa. Bayan sun sallamesa yajasu Sallar Asuban, duk wani k’aidojin karatu taji yana karewa, duk wani hukunce hukunce yana biya, a takaice sautin k’ira’ar sa ya burgeta ba kad’an ba saboda yadda yake da zak’in murya, sosai yayi impressing nata ashede ba jahili ta aura ba. Bayan sun sallame ya mik’e ze koma ya kwanta. “Anas” ta dakatar dashi da wuri. “What now Fannah? I want to sleep please.” “Babu kawai so nake na fad’a maka qira’arka tamin dad’i.” “Naji” yace sama sama yana k’ok’arin cire jallabiyar. Chan k’asa k’asa tace, “aini ban zata ka iya karatu bama.” Sekuwa yaji ta. “Kafiri ne ni ai dole kice baki zata na iya karatu ba. Toh in baki sani ba barin sanar dake yau cikin izu sittin na Qur’ani nayi talatin da biyu, kin gane? Ba jahili ne niba.” Mamaki sosai tajiyo, 32? Ta nanata a ranta. Amman shine bai aiki da ilimin Qur’anin nasa? Kuma besan hukunce hukunce ba a addinin muslinci. “Anas amman shine baka aiki da ilimin naka?” “Me ruwanki? My life is not your business, kuma ai ba ce miki nayi islamiyya nayi attending ba hadda ne, zallan Qur’ani da tajweed kawai akeyi sesa kiga ga bansan sauran religious stuffs d’innan ba time daya kamata nashiga islamiya nak’i ban shiga ba.” Sekuma yayi shiru “why am I even explaining these to you? Kin ga dama kice ban san komai ba game da addini keda kika sani sekita bragging dashi be damen ba kuma bare damen ba, allow me to sleep now, will you?” “Anas I’m sorry ba abinda nake nufi ba kenan also in aka idar da Sallan Asuba dama kowani Sallan ba direct akeson mutum ya tashi ba. Akwai morning azkar da akeyi wanda yake da falala sosai shima.” “Ohhhh!” Ya sa hannu cikin gashinsa a fusace yana hargitsawa. “Fannah please, please nace nan ba islamiyya bane kince inyi rakatainul~fajr nayi be isheki ba yanzu kuma azkhar kikeson sani yi? for goodness sake jiya bansamu nayi bacci ba, wannan mafarkin da kikayi duk ya bi ya tadda min hankali, haka kika hana ni bacci yanzu kuma dayakamata in kwanta shina kice barin yi ba?” Ya tambayeta a tsawace. Bata san lokacinda ta soma hawaye ba. “I’m sorry, Allah baka hak’uri.” Ta fad’a tana tare hawayenta. Kallonta yayi na ‘yan seconds tare da kawar dakansa, nan yacire jallabiyan ya haura kan gado. Sautin kukan tane ya hanasa sukuni, ya d’au pillow ya rufe kunnuwasa amman still yakasa bacci gashi kuma ita tak’i yin shiru besan ina ze kaita ba. Mutum da an masa magana se kuka sekace ‘yar yarinya. Ganin ba ubangiji se Allah ya taso daga kan gadon tare da zura jallabiyar sa, gabanta ya tako ahankali ya zauna tana azhkar nata da hisnul muslim nata ahannu tana kuka a hankali ko d’aga kai ta kallesa batai ba. Zama yayi a gefenta yana fuskantar ta. Littafin ya k’wace nan ne ta d’ago idanunta da suka soma canza launi. ‘I’m sorry’ yakeson fad’a mata but he can’t saboda girman kai instead yace, “they came out wrong, I don’t mean any of those words, kinji? Stop crying.” Yi tayi kamar bata ji sa ba “kabani littafi na” tace ba tare da ta d’aga ido ta kallesa ba. Shi mesa baya cewa sorry? Ita abu kad’an tayi masa zata ce sorry amman shi sede yace they came out wrong. “I said they came out wrong, ba haka naso su fito ba ko bakiji ba?” “Naji kabani littafi na toh.” “No zanyi Azkhar d’in.” Batasan lokacin da fuskarta ta sake ba, “zakayi?” ta tambayesa cike da jin dad’i. “Yes zanyi, show me the page.” Nan ya mi’ka mata bayan ta bud’e masa daga farin ta nunnuna masa. Kai ya gyad’a tare da amsa ya somayi. Kallonsa ta tsaya yi, ba k’aramin dad’i taji ba, a rayuwa batada burin da yafi ta shiryar da Anas, kuma alhamdulillah a hankali yana shiryuwan. Ya d’anyi nisa seya dakata tare da d’ago kansa nanne ya kama Fannah na kallonsa. ‘yar murmushi ya saki. “Kefa bara kiyi ba? Gashi gama seki bani, I’ll wait for you.” “No karka damu na iya a ka zanyi just use it.” Kai ya giad’a mata tare da mayar da hankalinsa kan littafin. Koda ta gama nata bata tashi ba seda ta jira ya gama shima sannan suka tashi atare. Jallabiyar yakuma cirewa ya haura kan gadon. So take tace masa ya koma wajen sa na jiya sede kuma ta tuna batada iko. D’ayan b’angaren ta nufa ta d’an ajiye pillows uku a tsakaninsu sa’annan ta kwanta itama daga chan nesa nesa. A hankali ya juyo yaga tana fuskantar d’ayan gefen ga kuma jera pillows d’in data sake a tsakaninsu. Kai kawai ya kad’a. “Da hijabin zaki kwanta?” Ya tambayeta. “Eh” ta basa amsa. “Yayi kyau.” Ahaka duk suka koma bacci ba su suka tashi ba se chan k’arfe 11:30AM nanma Anas ne ya tashi, idanunsa basu sauk’a a ko ina ba se akan kyakkyawar fuskar Fannah, tad’an gangaro kad’an zuwa wajen data yi katanga tsakaninsun. Wayarsa ya d’ago ya soma d’aukanta hoto yayi kusan guda ishirin yaga ta motsa k’afa da wuri wuri ya miyar ya cigaba da kallon ta. A lokaci d’aya kawai ta bud’e ido se karo taci dana Anas a kanta kunya yaji sosai a lokacin da ta tare fuskar tata da hijabi. Se k’arya ya mata wai; “ace warki kallon ki nake ne? Wannan uban minsharin da kiken ne ya tadani in the first place.” Fuskarta cikin hijabin tace, “ni bana minshari.” “Nikuma ba k’arya nake ba” yana kaiwa nan ya mik’e, towel da jakar wankansa ya ciro ya nufa toilet. Se ayanzu ta fiddo fuskar ta. Wajen akwatinta ta nufa ta ciro jakar wankanta da towel nata itama, takaici tajiyo data ga ‘yar tsawon towel d’in, ko gama kai tsakiyar cinyarta beyi ba, se yanzu ma take dana sanin d’auko towel nata na gida wanda yakai kusan guiwarta. Wayarta ta ciro takira gida suka gaisa da kowa da kowa se tsiya Afrah kemata amarya ansha amarchi, ya first night. Tsuka taja tare da kaste wayar. Bada dad’ewa ba Anas yafito tunda Fannah ta kafa idanunta akansa ta kasa d’aga wa. Ya d’aura towel d’in daidai iya V line na k’asansa, packs nasa da suke nan ’yan daidai suka sake bayyana. Wani k’aramin towel ne kuma rataye a wuyarsa wanda da d’ayan jelar yake goge gashin kansa daya jik’e jak’af yana sheqi. Wani haske skin nasa ya k’ara da d’igo d’igon ruwa kwance akai. Gashin jikinsa duk sun kwanta luf-luf, da fuskarsa ya bayyana kuwa, ruwa ke d’iga daga tip na hancinsa. “Kallon ya isa.” Yace da ita wani irin kunya taji kamar ta nitse k’asa wato tun d’azu ya karanchi kallonsa take kenan. Ya Salam!! Tace a ranta. “I get it I’m your husband you can stare at me amman banda irin kallon nan yayi yawa.” Fuskarta kawai ta rufe da hijabinta ta bi ta gefensa ta shiga bathroom d’in. Nan da nan ya shirya cikin sirinsa na safiya akullum ¾ wando da vest, gashin kansa yayi styling mekyau ya feffeshe da designer turarukansa tare da sa Bouzet agogonsa ya dake kan gado yana ‘yan latse latse a laptop nasa. “Ya Salam!” Fannah tasaki k’ara a cikin bayin kasancewar hijabinta daya fad’a tsundum cikin bathtub, kafin tace zata cire yariga yasha ruwa ya jik’e liqis. Kuka ne kawai batayi ba yanzu ya zatayi tafita da wannan gajeren towel dake jikin tan? Matsewa tatayi amman ina its not at all helping, tasa a haka kuma tana tsoron pneumonia nata karya tashi dan ba wai magani tasha ya mutu ba gabad’aya. Ganin ba ubangiji se Allah ta shanya hijabin a bayin, d’ayan k’aramin towel d’in ta d’aura a gashinta data wanke. Ta iso bakin k’ofar ta sake kallon jikinta kai bara ta iya fita haka ba gaban Anas, tsirecin yayi yawa ta baya kam ma inta tsuguna za’a iya ganinta. “Anas” ta kira sunansa daga cikin bayin ta yadda ze iya ji inhar yana cikin d’akin. Juyowa yayi yana kallon k’ofar. Me kuma takeso yanzu? Ya tambayi kansa. K’in amsawa yayi. “Anas are you there?” Nanma shiru yayi. Hamdala ta saki a ranta shikenan bayya ma d’akin barinyi sauri inje in zaro wani hijabin insa kafin ya dawo. Karap ta bud’e k’ofar tare da rufewa tana juyowa kawai taga Anas mik’e kan gado, mutuwar tsaye tayi a wajen... *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:54, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 5⃣7⃣ Kallonta Anas yake wane ze had’iyeta, ko kyafta ido ya kasa, numfashinsa ma gabad’ai yankewa yayi, in ya d’auka daga k’afafunta seya kai kanta ya tsaya sannan ya sake d’aukowa daga k’afafun nata. Yasha kallon mata kan bikini(pant da bra) amman ba wacce ta tab’a birkita masa lisafi kamar Fannah, she is just different in her own ways. Itako kasa koda motsi tayi she still can’t believe Anas ya ganta da towel. Idanunsu na had’uwa ta yi saurin sunkuyar da kanta a yayinda Anas ya soma faking tarin tsiya shi a dole wai ya shak’e ganin ta ba kaya disgusts him. Alokaci guda kuwa hankalinta ya dawo jikinta k’ofar ta soma jijjigawa ta baya tana k’ok’arin bud’ewa amman ta kasa dan yadda ta rikice. Idanunsa da ya kawar ya sake maido su kan ta a lokacin da take k’ok’arin bud’e k’ofar da sauri ta juya masa bayanta, data murd’a handle na k’ofar da k’arfi kuwa se ya bud’u. Kansa ya girgiza dan kawar da image na Fannah da towel daga k’wak’walwarsa. Wani takaici taji ya rufeta data sake kallon jikinta. K’ofar ta sake bud’ewa kad’an ta lek’a, k’afafunsa ta hango yana nan kan gadon har yanzu. Tunanin ya zata d’auko hijabinta take ganin batada wata mafitan dayafi ta kira Anas ta rok’esa kawai ta rufe ido ta kira san. “Ermm Anas.” Yana jinta yayi shiru har yanzu se yawo hotunan ta da towel yake masa akai. “Anas please nasan kana jina.” “Meh?” Ya tambaya a fusace. “Please hijabi na zaka ciro min cikin medium size akwati na maroon d’in.” Idanunsa ya miyar kan maroon akwatin nata sannan yace, “barin iya ba.” “Anas dan Allah kayi hak’uri please.” “Kifito ki d’auka da kanki.” “Anas banida kaya a jikina shiyasa please kayi hak’uri.” “Toh aini ba kallonki zanba.” “Nasani kawai ka taimaka please.” Kamar wanda bare tashi ba ya mik’e akwatin nata yaja ya bud’e to his suprise yaga na inner wears nata ne, ba komai banda bras da panties ciki. Daidai nan Fannah ta tuna ashe inner wears nata ke ciki, a red d’inne hijabanta ke ciki. “Anas hold on please kar ka bud’e bashi bane.” Inaaa aikin gama ya riga ya gama. Ko sauraranta beyi ba seda ya k’are wa inner wears natan kallo sannan yace, “nafasa kifito ki d’auka da kanki.” “Anas I’m sorry dan Allah cikin jan ne yana nan a gefe, please kaji?” Banza da ita yayi se chan daya ga dama ya bud’o jan ya ciro mata d’aya daga cikin hijaban nata. “Fito ki amsa gashi.” “Anas na d’au zaka kawo min ne fah.” “Cemin kikayi in ciro miki ba inkai miki ba, so kizo ki karb’a.” “Hausan nawa ne baka gane ba, ka mik’o min please.” Seda ya gama wasting mata lokaci sannan ya nufa wajen bathroom d’in tare da mik’a mata be jira ta gama karb’ewa ba ya sake k’iris ya rage ya fad’i a k’asa. “Thank you” tace masa a yayinda yayi banza da ita bayan tasa hijabin tafito kanta a sunkuye, akwatin inner wears natan taga a bud’e ga bressiers nata duk a k’asa duk Anas yayi watsi dasu. Shima kallon bressiers natan yake atare suka d’ago ido suna kallon juna cike da kunya ta kawar da kanta, a kunyace ta tsuguna tasoma tattara abinta duk inda ta nufa Anas na binta da kallo. Se guna guni take “kawai da ancewa mutum ya taimako da hijabi seya hargitsa wa mutum kaya.” “An hargitsan nan gaba seki na shiga da hijabinki in bakison ana ganin jikinki.” Shiru tayi batace masa komai ba, bayan ta gama had’a kayakin nata ta rufe, man shafawanta ta ciro tunanin ya zata shafa take chan ta juya taga Anas na kallonta mik’ewa tayi da nufin shiga bathroom ta yafe zataje ta shafa man acan. K’aramar tsuka yaja, “dawo ki shafa manki, I’m not interested in looking at your body.” Yana kaiwa nan ya tattara wayoyinsa ya fice ko ina zeje se Allah. “Tafi nono fari” tace chan k’asa k’asa yadda bare jita ba. Bayansa tabi ta sa lock a k’ofar, nan ta cire hijabin nata cikin kwanciyan hankali ta shafa manta ta bud’o akwatin kayakinta takaici ne ya rufeta kap ba atamfa english wears ne zalla ciki. “Afrah wallahi zan sab’a miki, seda nace miki karkisa min english wears ciki. Mschww!” Haka ba yadda ta iya ta ciro wani red highwaist skirt da white blouse had’ad’d’e ta ajiye a gefe, bayan tasa inner wears nata ta jawo skirt d’in bata gama sawa ba Anas ya murd’a hannunn k’ofar, jin a rufe ya fusata. “Fannah me na rufe ni a waje? Daga baki privacy seki kama kiyi locking d’akin?” “Toh ai na d’au ko fita zakayi.” “Toh ba fitan nayi ba, open the door.” “Barin sa kaya.” “Wai me zan kalla a jikinki? Open it.” A ranta tace ai wallahi sena gama sa kayan zan bud’e hakan kuwa tayi ignoring nasa seda ta gama sa kayan nata ta bud’e masa. Masifeta yayi niyan yi amman ganin yadda kayan jikinta ya mugun mata kyai seya fasa, yaji bayason sata kuka. Matsa masa tayi ya wuce ba tare da yace mata komai ba. Wajen kayakinta ta nufa ta since towel dake kantan a hankali take taje kanta har tagama da k’yar anzo wajen tayi tayi ta kama ta kasa koda ta kama se ya sake fita. Kamar wacce zatayi kuka ta juyo tana kallon Anas, kallon nata yake shima ganin ta juyo yayi saurin maida kallonsa kan wayarsa. A hankali ta tako zuwa gabansa ta tsaya “Anas help me pack my hair please.” Banza yayi da ita “kaji Anas please?” Nanne ya d’ago blue eyes nasa yana kallonta, irin kallon data tsana kenan, kanta ta sunkuyar chan ta d’ago ta ga still kallonta Anas yake ko kunya ya kawar da kansa ma be ba. “Anas kabar kallo na haka mana, in ni ke kallonka seka ce na fiye kallo dayawa, nima banason kallon ya isa please ka kama min. Kaji?” Nanma bece mata komai ba. Ganin baida niyyan kama mata ta juya zata tafi hannunta yajawo seda ta fad’o jikinsa nauyinta kan cinyarsa, hannunta ta zagaya a wuyansa dan balancing kanta. K’ara ta saki take ya aza hannunsa kan lips nata “shhh!” Shirun tayi kum. Kallon cikin idanun juna suke na kusan minti biyu sannan ta d’aga kanta daga jikinsa, murmushi ya saki ta gefe d’aya saboda yasan yadda d’an wannan abu yayi affecting Fannah. Hannunta ya rik’i kafin ta fice, “tsaya mana ko bakiya so in kama miki gashin ne?” “Banaso I’ll manage sakemin hannu Mr. Fauzi.” K’in sake mata hannun yayi, wayansa ya ajiye tare da mik’ewa. Hannunta me ribbon d’in ya kama shima tare da zare ribbon d’in. Fannah kad’ai tasan irin shock da takeji, akoda yaushe Anas ya tab’a ta wani erin electrification takeji a ajikinta wanda battaso. A hankali ya sake duka hannun nata ya soma packing gashin natan, a hankali har ya kama waje guda. Hannunta tasa zata tattare jelar a yayinda ya kama hannun nata “kibarshi haka kinfi kyau.” “But An-” “Lets not argue haka yafi kyau, karki tab’a kinji?” Kai kawai ta gyad’a masa tareda k’watan hannunta a hankali, binta da kallo yake har ta nufa wajen kujera ta zauna jin idanunsa akanta tak’i d’aga kanta. Chan da zaman shirun ya isheta tace, “Anas ba breakfast ne?” “Jiya danace kici abinci me kika cemin? you are not hungry koba haka ba? Ba bareakfast ‘cause bana jin yunwa ni se lunch.” Fuska ta maraice “Anas yunwa nakeji.” “Kijira zuwa anjima se muci lunch.” Bata sake ce masa komai ba ta mik’e kan 3 seater’n tare da juya masa baya. Yunwa sosai takeji har wani kuka cikinta yakeyi. Knocking akayi bisa k’ofar nasu nan ya mik’e abincinsu aka kawo musu bayan ya amsa ya ajiye kan table d’in har ayanzu Fannah batasan meke faruwa ba. Plate natan ya b’oye k’ark’ashin gado. Yana bud’e nasan k’amshin sardine sauce da chips d’in ya cika d’akin, Fannah bata san lokacin da ta juyo tana kallon sa ba, har d’igan miyau takeyi gawani kukan da cikinta keyi. Seda ya tabbata tana ganinsa yakai spoon d’aya baki se exxagerating dad’in abincin yake. “Anas ni banda ni ne? Ina nawa?” “Babu” yabata takaicaccen amsa. “Kamar ya babu?” “Jiya danace kici abinci ba k’in ci kikayi ba?” “Anas ba ya wuce ba? Nan gaba barin sake ba, please ina plate d’ina?” “You promise? Nan gaba nace kici abinci zakici?” Kai ta gyad’a a hankali. “Good” hannu yasa k’ark’ashin gadon yaciro mata plate natan. “Come over lets eat.” Ba musu ta tashi taje ta samesa bayan ya mik’a mata plate natan ta zauna gefe dashi ahaka suka samu sukayi breakfast nasu. Kallonta yake yadda take ta cin abincin ba makawa gaskia yunwa yacita da yawa, bayan da ta gama ya tambayeta “a k’ara miki?” Kai ta gyad’a a hankali plate nasa ya mik’a mata. “Kaifa ka k’oshi?” Kai ya gyad’a mata nan da nan ta d’ura nasan cikinta se ayanzu ta jita dam. Lokacin Sallah ya riga yayi nan ta fad’a bayi tayi alwala shima haka sannan ya jasu Sallah bayan da suka idar ya sake feshe jikinsa da turare binsa kawai take da kallo seda yazo fita takira sunansa ganin baida niyyan fad’a mata inda zasa. “Anas.” Chak ya tsaya “wani abu ne?” Ya tambayeta bayan ya bud’e k’ofar. “Nace ina zakaje?” “Toh wifey kishi ne ya motsa?” “Nifa ba kishin ka nake ba.” “Toh why asking? Karki damu ba wajen wata zanje ba” “Toh ni ina ruwa na? Inma chan zakaje Allah kare ni I thought ko zaka sauk’eni a gida ne.” “Kin tab’a ganin inda amarya ta fita?” “Anas zaman nan d’in ba dad’i.” Wani murmushin tsiya ya saki, “just say it you are gonna miss me, karki damu I won’t take long yanzu zan dawo.” Bejira jin me zatace ba ya rufe k’ofar. ‘Yar tsukar ta taja tare da hayewa kan gadon, game na candy crush ta hau yi batasan seda bacci yayi gaba da ita ba. _40 minutes later..._ A nitse ya bud’e k’ofar kamar ko yasan tana bacci. Ledar chocolates da ice cream daya siyo musu ya bud’e fridge d’in yasa ciki sannan ya nufa kan gadon inda take kwance bayan ya zauna gefenta ya zura mata ido. wayarta dake kwance a gefenta ya zaro yayi quitting game d’in. Hannu yasa a fuskarta a hankali ta yadda bare farkar da ita ba, gashin dake kwance kai ya d’ad’d’aga sannan ya jawo bargo ya rufeta. **** Seda La’asar ya tada ta suka idar da Sallah tare da musu ordering abinci, suna cikin ci aka yi knocking a k’ofa “get it” yache mata ba musu ta mik’e ta bud’e kad’an daga photo album na bikinsu ne aka kawo musu. Bayan ta amsa ta masa godiya. “Mugani” Anas yace. “Nima ingani mana.” “I’m your husband you follow my instructions so bani.” Kallo ta galla masa “awww ni kike harara?” “Bafa harararka nake ba.” Nan ta mik’a masa. Na english dinner’n su ya soma bud’e “wow!” Tace cike da jin dad’i ganin yadda tayi kyau a hoton. “Wow me or you?” “Ni de, ni ba kai nake kallo ba.” “Da banga idanunki kan fuska na bane seki fad’a min maganan banza.” “Nide ba kai nake kallo ba.” Ignoring nata yayi suka cigaba da kallon pictures d’in se anzo page dayaga tayi kyau se ya wani wuce da wuri wuri in akazo inda yayi kyau kamar ba gobe kuma seya tsaya yana admiring kansa. K’ananun tsuka take ja. “Toh Anas a wuce page d’innan mana munfi minti uku fa muna kallo.” “In kin gaji seki tashi, thank god I’m handsome and admit it you enjoy looking at my handsome face.” “Nide I don’t enjoy.” D’ayan page d’in ya juya ganin tayi kyau yayi sauri ya juya “Anas ka tsaya mana muga nan d’in.” “Keda wa? Page d’in beyi kyau ba bara’a kalla ba.” Bata sake ce masa komai ba ya juya next page d’in. Babban hotonsa da Fannah ne kad’ai a page d’in wanda tabar wani duk abinda takeyi tana kallonsa zallah. Kunya taji sosai ita kanta bata san ya akayi hakan ta faru ba. Hannu tasa ta rufe. “Me haka? D’aga hannun mana.” “A’a Anas dan Allah ka juya.” “Nak’i, ni nace ki tsaya kallo na awajen d’aga hannun. Kinga I can’t touch you saboda a contract namu ba body contact, d’aga hannun ki.” Tana d’agawa ta bar wajen. Dariya yakeson yi amman bayason ta raina sa. Tana kallonsa ya d’au hoton a wayarsa. ***** Bayan sun idar da Sallan Isha sukaci abinci bayi Fannah ta fad’a ta watsa ruwa a cikinsa ta canza kaya tana fitowa kamar jiya ta jera pillows tsakaninsu. Kallonta kawai yayi tare da kad’a kai bayan data kwanta yaje ya watsa ruwan shima. Pillow d’aya ya zaro ya koma kan cushion daya kwanta jiya ya mik’e akai bada jimawa ba shima yayi baccin. Kamar jiya yau ma ta farka da ihu nan shima Anas ya tashi. Kukan da takeyi yau kamar ma yafi na jiya. Kamar jiya haka ya samu yayi calming nata da k’yar tabar kukan sede b’arin da take har yanzu. “Toh sakeni zan koma in kwanta.” “A’a dan Allah Anas karka tafi wallahi mutumin ze dawo.” “Bare dawo ba, sakeni toh.” Gangamesa ta sake tana girgiza kai. “Haka kikeson mu raya daren a zaune?” “A’a nide kawai karka tafi dan Allah” ta rok’esa cikin sautin kuka. “Toh ka kwanta anan.” “A’a achan zan kwanta ba kece sarkin yin katanga da pillow ba? Kwanta abinki zan kwana achan nima.” “A’a zan cire dan Allah karka tafi Anas.” “Nifa barin kwana nan ba sekin cire pillows d’in da kanki.” “Naji zan cire” hannunsa ta kama gudun kar ya gudu tayi watsi da pillows d’in tas. “Nacire dan Allah don’t leave me, inma zaka barni ka kira Mami tazo.” “Naji I won’t leave you barin d’auko pillow na.” “A’a ga nawa dan Allah kar ka tafi.” Murmushi ya saki. “Toh matsa ciki” ba musu ta matsa kan pillon nata ya kwanta. “Azaune zakiyi baccin ne?” Kai ta girgiza. “Kicire hijabin toh. Wai ma bakiya jin zufan da kikeyi ne?” Nanma kai ta girgiza “fine zan koma kan kushion na kwanta.” “Anas dan Allah karka tafi” har yanzu bata bar b’arin da take ba. “Toh kicire you are sweating.” A hanakli ta yaye hijabin ta shiga kare k’irjinta. Kansa ya kawar daga gareta “seki kwanta.” Pillow d’aya taja ta matso dashi kusa da nasa duk tsoro yabi ya ratsa ta. Bayan minti biyar Anas ya juya yaga har yanzu batai bacci ba se b’ari take tana had’a gumi sekuma ta basa tausayi. “Kin kasa bacci neh?” Ya tambayeta cike da damuwa. Kai ta gyad’a a hankali. “I’m here kinji? Ba mutumin daze zo, ina zuwa.” Hannunsa ta rik’o “Anas ina zakaje?” “Bathroom ya amsata.” “Dan Allah kar ka tafi please.” “Fannah I want to use the bathroom ba tafiya zan yi ba, kibani just a minute.” Ai sam tak’i sake hannun nasa. Haka har bakin bathroom d’in tabi sa tana jiran fitowarsa se waiwaye waiwaye take kar mutumin yazo mata. “Anas kayi sauri dan Allah kaji?” Se buga k’ofar takeyi sam tak’i barinsa yagama biyan buk’antansa. Yana fitowa ta kama hannunsa ahaka suka isa kan gadon suka kwanta. Ta sake masa hannu ma tak’i. Ahaka har tayi bacci, hannun nasa ya gwada cirewa daga nata amman gam ta matse cikin nata bibbiyu... *© miemiebee* beeenovels.mywapblog.com [12:55, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: [3:59PM, 8/29/2016] Rukayya: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 5⃣8⃣ Kallonta Anas yake wane ze had’iyeta, ko kyafta ido ya kasa, numfashinsa ma gabad’ai yankewa yayi, in ya d’auka daga k’afafunta seya kai kanta ya tsaya sannan ya sake d’aukowa daga k’afafun nata. Yasha kallon mata kan bikini(pant da bra) amman ba wacce ta tab’a birkita masa lisafi kamar Fannah, she is just different in her own ways. Itako kasa koda motsi tayi she still can’t believe Anas ya ganta da towel. Idanunsu na had’uwa ta yi saurin sunkuyar da kanta a yayinda Anas ya soma faking tarin tsiya shi a dole wai ya shak’e ganin ta ba kaya disgusts him. Alokaci guda kuwa hankalinta ya dawo jikinta k’ofar ta soma jijjigawa ta baya tana k’ok’arin bud’ewa amman ta kasa dan yadda ta rikice. Idanunsa da ya kawar ya sake maido su kan ta a lokacin da take k’ok’arin bud’e k’ofar da sauri ta juya masa bayanta, data murd’a handle na k’ofar da k’arfi kuwa se ya bud’u. Kansa ya girgiza dan kawar da image na Fannah da towel daga k’wak’walwarsa. Wani takaici taji ya rufeta data sake kallon jikinta. K’ofar ta sake bud’ewa kad’an ta lek’a, k’afafunsa ta hango yana nan kan gadon har yanzu. Tunanin ya zata d’auko hijabinta take ganin batada wata mafitan dayafi ta kira Anas ta rok’esa kawai ta rufe ido ta kira san. “Ermm Anas.” Yana jinta yayi shiru har yanzu se yawo hotunan ta da towel yake masa akai. “Anas please nasan kana jina.” “Meh?” Ya tambaya a fusace. “Please hijabi na zaka ciro min cikin medium size akwati na maroon d’in.” Idanunsa ya miyar kan maroon akwatin nata sannan yace, “barin iya ba.” “Anas dan Allah kayi hak’uri please.” “Kifito ki d’auka da kanki.” “Anas banida kaya a jikina shiyasa please kayi hak’uri.” “Toh aini ba kallonki zanba.” “Nasani kawai ka taimaka please.” Kamar wanda bare tashi ba ya mik’e akwatin nata yaja ya bud’e to his suprise yaga na inner wears nata ne, ba komai banda bras da panties ciki. Daidai nan Fannah ta tuna ashe inner wears nata ke ciki, a red d’inne hijabanta ke ciki. “Anas hold on please kar ka bud’e bashi bane.” Inaaa aikin gama ya riga ya gama. Ko sauraranta beyi ba seda ya k’are wa inner wears natan kallo sannan yace, “nafasa kifito ki d’auka da kanki.” “Anas I’m sorry dan Allah cikin jan ne yana nan a gefe, please kaji?” Banza da ita yayi se chan daya ga dama ya bud’o jan ya ciro mata d’aya daga cikin hijaban nata. “Fito ki amsa gashi.” “Anas na d’au zaka kawo min ne fah.” “Cemin kikayi in ciro miki ba inkai miki ba, so kizo ki karb’a.” “Hausan nawa ne baka gane ba, ka mik’o min please.” Seda ya gama wasting mata lokaci sannan ya nufa wajen bathroom d’in tare da mik’a mata be jira ta gama karb’ewa ba ya sake k’iris ya rage ya fad’i a k’asa. “Thank you” tace masa a yayinda yayi banza da ita bayan tasa hijabin tafito kanta a sunkuye, akwatin inner wears natan taga a bud’e ga bressiers nata duk a k’asa duk Anas yayi watsi dasu. Shima kallon bressiers natan yake atare suka d’ago ido suna kallon juna cike da kunya ta kawar da kanta, a kunyace ta tsuguna tasoma tattara abinta duk inda ta nufa Anas na binta da kallo. Se guna guni take “kawai da ancewa mutum ya taimako da hijabi seya hargitsa wa mutum kaya.” “An hargitsan nan gaba seki na shiga da hijabinki in bakison ana ganin jikinki.” Shiru tayi batace masa komai ba, bayan ta gama had’a kayakin nata ta rufe, man shafawanta ta ciro tunanin ya zata shafa take chan ta juya taga Anas na kallonta mik’ewa tayi da nufin shiga bathroom ta yafe zataje ta shafa man acan. K’aramar tsuka yaja, “dawo ki shafa manki, I’m not interested in looking at your body.” Yana kaiwa nan ya tattara wayoyinsa ya fice ko ina zeje se Allah. “Tafi nono fari” tace chan k’asa k’asa yadda bare jita ba. Bayansa tabi ta sa lock a k’ofar, nan ta cire hijabin nata cikin kwanciyan hankali ta shafa manta ta bud’o akwatin kayakinta takaici ne ya rufeta kap ba atamfa english wears ne zalla ciki. “Afrah wallahi zan sab’a miki, seda nace miki karkisa min english wears ciki. Mschww!” Haka ba yadda ta iya ta ciro wani red highwaist skirt da white blouse had’ad’d’e ta ajiye a gefe, bayan tasa inner wears nata ta jawo skirt d’in bata gama sawa ba Anas ya murd’a hannunn k’ofar, jin a rufe ya fusata. “Fannah me na rufe ni a waje? Daga baki privacy seki kama kiyi locking d’akin?” “Toh ai na d’au ko fita zakayi.” “Toh ba fitan nayi ba, open the door.” “Barin sa kaya.” “Wai me zan kalla a jikinki? Open it.” A ranta tace ai wallahi sena gama sa kayan zan bud’e hakan kuwa tayi ignoring nasa seda ta gama sa kayan nata ta bud’e masa. Masifeta yayi niyan yi amman ganin yadda kayan jikinta ya mugun mata kyai seya fasa, yaji bayason sata kuka. Matsa masa tayi ya wuce ba tare da yace mata komai ba. Wajen kayakinta ta nufa ta since towel dake kantan a hankali take taje kanta har tagama da k’yar anzo wajen tayi tayi ta kama ta kasa koda ta kama se ya sake fita. Kamar wacce zatayi kuka ta juyo tana kallon Anas, kallon nata yake shima ganin ta juyo yayi saurin maida kallonsa kan wayarsa. A hankali ta tako zuwa gabansa ta tsaya “Anas help me pack my hair please.” Banza yayi da ita “kaji Anas please?” Nanne ya d’ago blue eyes nasa yana kallonta, irin kallon data tsana kenan, kanta ta sunkuyar chan ta d’ago ta ga still kallonta Anas yake ko kunya ya kawar da kansa ma be ba. “Anas kabar kallo na haka mana, in ni ke kallonka seka ce na fiye kallo dayawa, nima banason kallon ya isa please ka kama min. Kaji?” Nanma bece mata komai ba. Ganin baida niyyan kama mata ta juya zata tafi hannunta yajawo seda ta fad’o jikinsa nauyinta kan cinyarsa, hannunta ta zagaya a wuyansa dan balancing kanta. K’ara ta saki take ya aza hannunsa kan lips nata “shhh!” Shirun tayi kum. Kallon cikin idanun juna suke na kusan minti biyu sannan ta d’aga kanta daga jikinsa, murmushi ya saki ta gefe d’aya saboda yasan yadda d’an wannan abu yayi affecting Fannah. Hannunta ya rik’i kafin ta fice, “tsaya mana ko bakiya so in kama miki gashin ne?” “Banaso I’ll manage sakemin hannu Mr. Fauzi.” K’in sake mata hannun yayi, wayansa ya ajiye tare da mik’ewa. Hannunta me ribbon d’in ya kama shima tare da zare ribbon d’in. Fannah kad’ai tasan irin shock da takeji, akoda yaushe Anas ya tab’a ta wani erin electrification takeji a ajikinta wanda battaso. A hankali ya sake duka hannun nata ya soma packing gashin natan, a hankali har ya kama waje guda. Hannunta tasa zata tattare jelar a yayinda ya kama hannun nata “kibarshi haka kinfi kyau.” “But An-” “Lets not argue haka yafi kyau, karki tab’a kinji?” Kai kawai ta gyad’a masa tareda k’watan hannunta a hankali, binta da kallo yake har ta nufa wajen kujera ta zauna jin idanunsa akanta tak’i d’aga kanta. Chan da zaman shirun ya isheta tace, “Anas ba breakfast ne?” “Jiya danace kici abinci me kika cemin? you are not hungry koba haka ba? Ba bareakfast ‘cause bana jin yunwa ni se lunch.” Fuska ta maraice “Anas yunwa nakeji.” “Kijira zuwa anjima se muci lunch.” Bata sake ce masa komai ba ta mik’e kan 3 seater’n tare da juya masa baya. Yunwa sosai takeji har wani kuka cikinta yakeyi. Knocking akayi bisa k’ofar nasu nan ya mik’e abincinsu aka kawo musu bayan ya amsa ya ajiye kan table d’in har ayanzu Fannah batasan meke faruwa ba. Plate natan ya b’oye k’ark’ashin gado. Yana bud’e nasan k’amshin sardine sauce da chips d’in ya cika d’akin, Fannah bata san lokacin da ta juyo tana kallon sa ba, har d’igan miyau takeyi gawani kukan da cikinta keyi. Seda ya tabbata tana ganinsa yakai spoon d’aya baki se exxagerating dad’in abincin yake. “Anas ni banda ni ne? Ina nawa?” “Babu” yabata takaicaccen amsa. “Kamar ya babu?” “Jiya danace kici abinci ba k’in ci kikayi ba?” “Anas ba ya wuce ba? Nan gaba barin sake ba, please ina plate d’ina?” “You promise? Nan gaba nace kici abinci zakici?” Kai ta gyad’a a hankali. “Good” hannu yasa k’ark’ashin gadon yaciro mata plate natan. “Come over lets eat.” Ba musu ta tashi taje ta samesa bayan ya mik’a mata plate natan ta zauna gefe dashi ahaka suka samu sukayi breakfast nasu. Kallonta yake yadda take ta cin abincin ba makawa gaskia yunwa yacita da yawa, bayan da ta gama ya tambayeta “a k’ara miki?” Kai ta gyad’a a hankali plate nasa ya mik’a mata. “Kaifa ka k’oshi?” Kai ya gyad’a mata nan da nan ta d’ura nasan cikinta se ayanzu ta jita dam. Lokacin Sallah ya riga yayi nan ta fad’a bayi tayi alwala shima haka sannan ya jasu Sallah bayan da suka idar ya sake feshe jikinsa da turare binsa kawai take da kallo seda yazo fita takira sunansa ganin baida niyyan fad’a mata inda zasa. “Anas.” Chak ya tsaya “wani abu ne?” Ya tambayeta bayan ya bud’e k’ofar. “Nace ina zakaje?” “Toh wifey kishi ne ya motsa?” “Nifa ba kishin ka nake ba.” “Toh why asking? Karki damu ba wajen wata zanje ba” “Toh ni ina ruwa na? Inma chan zakaje Allah kare ni I thought ko zaka sauk’eni a gida ne.” “Kin tab’a ganin inda amarya ta fita?” “Anas zaman nan d’in ba dad’i.” Wani murmushin tsiya ya saki, “just say it you are gonna miss me, karki damu I won’t take long yanzu zan dawo.” Bejira jin me zatace ba ya rufe k’ofar. ‘Yar tsukar ta taja tare da hayewa kan gadon, game na candy crush ta hau yi batasan seda bacci yayi gaba da ita ba. _40 minutes later..._ A nitse ya bud’e k’ofar kamar ko yasan tana bacci. Ledar chocolates da ice cream daya siyo musu ya bud’e fridge d’in yasa ciki sannan ya nufa kan gadon inda take kwance bayan ya zauna gefenta ya zura mata ido. wayarta dake kwance a gefenta ya zaro yayi quitting game d’in. Hannu yasa a fuskarta a hankali ta yadda bare farkar da ita ba, gashin dake kwance kai ya d’ad’d’aga sannan ya jawo bargo ya rufeta. **** Seda La’asar ya tada ta suka idar da Sallah tare da musu ordering abinci, suna cikin ci aka yi knocking a k’ofa “get it” yache mata ba musu ta mik’e ta bud’e kad’an daga photo album na bikinsu ne aka kawo musu. Bayan ta amsa ta masa godiya. “Mugani” Anas yace. “Nima ingani mana.” “I’m your husband you follow my instructions so bani.” Kallo ta galla masa “awww ni kike harara?” “Bafa harararka nake ba.” Nan ta mik’a masa. Na english dinner’n su ya soma bud’e “wow!” Tace cike da jin dad’i ganin yadda tayi kyau a hoton. “Wow me or you?” “Ni de, ni ba kai nake kallo ba.” “Da banga idanunki kan fuska na bane seki fad’a min maganan banza.” “Nide ba kai nake kallo ba.” Ignoring nata yayi suka cigaba da kallon pictures d’in se anzo page dayaga tayi kyau se ya wani wuce da wuri wuri in akazo inda yayi kyau kamar ba gobe kuma seya tsaya yana admiring kansa. K’ananun tsuka take ja. “Toh Anas a wuce page d’innan mana munfi minti uku fa muna kallo.” “In kin gaji seki tashi, thank god I’m handsome and admit it you enjoy looking at my handsome face.” “Nide I don’t enjoy.” D’ayan page d’in ya juya ganin tayi kyau yayi sauri ya juya “Anas ka tsaya mana muga nan d’in.” “Keda wa? Page d’in beyi kyau ba bara’a kalla ba.” Bata sake ce masa komai ba ya juya next page d’in. Babban hotonsa da Fannah ne kad’ai a page d’in wanda tabar wani duk abinda takeyi tana kallonsa zallah. Kunya taji sosai ita kanta bata san ya akayi hakan ta faru ba. Hannu tasa ta rufe. “Me haka? D’aga hannun mana.” “A’a Anas dan Allah ka juya.” “Nak’i, ni nace ki tsaya kallo na awajen d’aga hannun. Kinga I can’t touch you saboda a contract namu ba body contact, d’aga hannun ki.” Tana d’agawa ta bar wajen. Dariya yakeson yi amman bayason ta raina sa. Tana kallonsa ya d’au hoton a wayarsa. ***** Bayan sun idar da Sallan Isha sukaci abinci bayi Fannah ta fad’a ta watsa ruwa a cikinsa ta canza kaya tana fitowa kamar jiya ta jera pillows tsakaninsu. Kallonta kawai yayi tare da kad’a kai bayan data kwanta yaje ya watsa ruwan shima. Pillow d’aya ya zaro ya koma kan cushion daya kwanta jiya ya mik’e akai bada jimawa ba shima yayi baccin. Kamar jiya yau ma ta farka da ihu nan shima Anas ya tashi. Kukan da takeyi yau kamar ma yafi na jiya. Kamar jiya haka ya samu yayi calming nata da k’yar tabar kukan sede b’arin da take har yanzu. “Toh sakeni zan koma in kwanta.” “A’a dan Allah Anas karka tafi wallahi mutumin ze dawo.” “Bare dawo ba, sakeni toh.” Gangamesa ta sake tana girgiza kai. “Haka kikeson mu raya daren a zaune?” “A’a nide kawai karka tafi dan Allah” ta rok’esa cikin sautin kuka. “Toh ka kwanta anan.” “A’a achan zan kwanta ba kece sarkin yin katanga da pillow ba? Kwanta abinki zan kwana achan nima.” “A’a zan cire dan Allah karka tafi Anas.” “Nifa barin kwana nan ba sekin cire pillows d’in da kanki.” “Naji zan cire” hannunsa ta kama gudun kar ya gudu tayi watsi da pillows d’in tas. “Nacire dan Allah don’t leave me, inma zaka barni ka kira Mami tazo.” “Naji I won’t leave you barin d’auko pillow na.” “A’a ga nawa dan Allah kar ka tafi.” Murmushi ya saki. “Toh matsa ciki” ba musu ta matsa kan pillon nata ya kwanta. “Azaune zakiyi baccin ne?” Kai ta girgiza. “Kicire hijabin toh. Wai ma bakiya jin zufan da kikeyi ne?” Nanma kai ta girgiza “fine zan koma kan kushion na kwanta.” “Anas dan Allah karka tafi” har yanzu bata bar b’arin da take ba. “Toh kicire you are sweating.” A hanakli ta yaye hijabin ta shiga kare k’irjinta. Kansa ya kawar daga gareta “seki kwanta.” Pillow d’aya taja ta matso dashi kusa da nasa duk tsoro yabi ya ratsa ta. Bayan minti biyar Anas ya juya yaga har yanzu batai bacci ba se b’ari take tana had’a gumi sekuma ta basa tausayi. “Kin kasa bacci neh?” Ya tambayeta cike da damuwa. Kai ta gyad’a a hankali. “I’m here kinji? Ba mutumin daze zo, ina zuwa.” Hannunsa ta rik’o “Anas ina zakaje?” “Bathroom ya amsata.” “Dan Allah kar ka tafi please.” “Fannah I want to use the bathroom ba tafiya zan yi ba, kibani just a minute.” Ai sam tak’i sake hannun nasa. Haka har bakin bathroom d’in tabi sa tana jiran fitowarsa se waiwaye waiwaye take kar mutumin yazo mata. “Anas kayi sauri dan Allah kaji?” Se buga k’ofar takeyi sam tak’i barinsa yagama biyan buk’antansa. Yana fitowa ta kama hannunsa ahaka suka isa kan gadon suka kwanta. Ta sake masa hannu ma tak’i. Ahaka har tayi bacci, hannun nasa ya gwada cirewa daga nata amman gam ta matse cikin nata bibbiyu... *© miemiebee* b[truncated by WhatsApp] [4:32PM, 8/29/2016] Rukayya: sorry ashe 57 suka sama number 58 [12:55, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 5⃣8⃣ *A/N* *ASSALAMU ALAIKUM MASU KARATU INASON YIN AMFANI DA WANNAN DAMA DAN BAKU HAK’URI GABAD’AYA GAME DA RASHIN POSTING DA BAN SAMU NAYI BA JIYA, NAGAMA TYPING UNFORTUNATELY SEYA GOGE KANSA BEFORE I COULD GET TO SAVE IT.* *SECONDLY, TO ALL MY BLOG READERS INA ME BAKU HAK’URI DA PROMBLEM DA BLOG NAWAN YASAMU, I’M STILL WORKING ON IT. I HOPE ZAKU CIGABA DA SAMUN CONTINUATION D’IN WANNNAN LITTAFI WAJEN OTHERS KU KARANTA KAFIN AGAMA GYARAN, INHAR HAKAN BE YUWU BA KUWA NAKEGA NEW BLOG ZAN BUD’E WANDA ZAN SANAR DAKU NEW ADDRESS D’IN WHEN AM DONE.* *LASTLY TO ALL MY FANS DA SUKA MIN MAGANA TA PRIVATE JIYA DA KUMA YAU DA SAFE KUYI HAK’URI BARIN IYA SAMUN DAMA INYI REPLYING MESSAGES NAKU GABAD’AI BA SOBADA YAWAN CHATS SESA NA GOGE DUKA KAWAI, IN DAMA DAN GAISUWA NE TOH MIEMIEBEE NAGODIYA, INKUMA DAN JIN DALILIN DAYA HANANI POSTING JIYA NE GASHI NAYI EXPLAINING, IN KUMA SAB’ANIN HAKA, YOU CAN PING ME AGAIN.* *THANK YOU SO MUCH FOR YOUR LOVE AND SUPPORT. MIEMIEBEE LOVES YOU SO VERY MUCH* Cikin baccin tace, “Anas dan Allah kar ka tafi please.” Alokaci guda kuma yaji wani irin tausayinta ya kamasa, bacci take amman idanunta basu bar zuban hawaye ba. D’ayan hannunsa yasa ya share mata hawayer. “Bar kuka kinji? I’m here.” Hannunsa ya raba da nata na k’arfi ganin yadda ta kama nasa gagam. Firgit ta tashi tana hawaye “Anas please don’t go.” “Ba tafiya zanyi ba Fannah” ya sanar da ita a lokacin dayake k’ok’arin kwantar da ita kan k’irjinsa. Bayan ya kwantar da itan ya soma shafa bayanta yana kwantar mata da hankali. “I’m here ba tafiya zanyi ba kinji?” Kai ta gyad’a cikin tsoro. Chan yaji nauyinta ya dad’u a kansa, beyi yunk’urin d’agata ba, barinta yayi ta cigaba da baccin gudun kar ya tayarda ita. Tunanin me yake sata mafarki haka yake. Waye mutumin? Mesa take kuka? Me ya tab’a mata? Me kuma take tsoron ze sake yi mata? Mesa kullum take irin mafarkin? For how long take erin wannan mafarkin dayake mugun tsorata ta haka? Me wannan mutumi ya mata? Har bacci yayi gaba dashi besamu amsoshi ga wad’annan tambayoyi ba. Asubar fari Fannah ta tashi a hankali ta bud’e idanunta, hannunta taja daga kan cikin Anas a hankali. Ta rasa meke sata mafarkin mutumin kullum kwana biyu, a da ne da abin yafaru take mafarkin kullum but as days passed by tadena yi kullum setayi kwana uku ma wani sa’in batayi ba amman tunda tayi aure takeyi kullum yanzu, kuma na yanzu yafi nada kayan ban tsoro. Me dalili? Bata kawo wani tunani a ranta ba ta miqe tayi alwala har a yanzu tsoro takeji mafarkin jiya yafi kowanne abin tsoro bayan tafito ta yi musu shimfid’a sannan ta tada Anas. Sun idar da Sallansu sunyi Azkhar suka koma kan gado. Pillow’nta ta matsar baya daga nasa tare da duk’unk’unewa cikin hijabinta tana kallon d’ayan side d’in. Anas ya karanchi hakan, yagano har yanzu tsoro takeji ga rashin maganar da takeyi yau kamar ba ita ba. Tausayinta yasake ji ya kama sa making him so anxious jin labarin mafarkin nata. “Fannah” ya kira sunanta cikin wani irin salo. “Na’am” ta amsa ba tare da ta juyo ba. “Are you still scared?” Kai ta girgiza masa tana matse ‘yar k’wallarta batadamu ko yana kallonta ko a’a ba. “I’m here for you kinji? Kibarjin tsoro ba mutumin da ze zo.” Yayi assuring nata. Kai ta gyad’a. “For how many months now kike mafarkin?” Bata masa k’arya ba tace, “7 years now.” 7 years? Ya nanata a ransa, Allah sarki poor Fannah. “Turn and look at me.” Ya buk’ace ta. Ba gardama ta juyo hawayen da take ta k’ok’arin matsewa ne suka soma gangara. Hannunsa ya bud’a mata “come.” Matsowa tayi kusa dashi cije da tsoro, kanta ya aza a kan k’irjinsa. “Everything is going to be alright kinji? Stop crying.” Hannu yasa ya share mata hawayen. “Do you want to talk about the dream?” Kai kawai ta girgiza masa. “Even now that I’m your husband?” Ya tambaya cikin wani irin demanding salo. Kuka ta fashe da, “Anas nima bansani ba anytime na kwanta kawai se inji wai wani mutumi yazo yana bina ze gudu dani.” Ta masa k’arya dan battason sanar dashi sirrinta. “Shhhh! Is okay bar kukan, lets sleep.” Hannunta ta zagaya akan cikinsa ayayinda yake ta shafa bayanta har tayi bacci. **** Da misalin k’arfe 10:00AM Fannah na zaune shiru kan cushion, game data saba yin ma tak’iyi yau. Yanzu suka gama breakfast da Anas. Observing nata yake tun da suka tashi haka take ta acting strange, ya rasa me ze mata koda ya mata magana amsarta befin ‘eh’ ko ‘a’a’. “Fannah” ya kira sunanta a nitse. “Na’am” ta d’ago kai tana kallonsa. “Kinason kifita yau?” Kai ta girgiza masa da nufin a’a sekace ba ita ba.. “In kaiki wajen Mami?” Batasan lokacin da ta saki murmushi ba “eh” ta basa amsa cike da jin dad’i. “Lets go then.” Dama abaya ne a jikinta, gyalenta ta d’auka tayi rolling tare da feffeshe jikinta da ture haka shima Anas d’in. Hannunta rik’e cikin nasa suka fice motan ma shiya bud’e mata da kansa ya rufe bayan ta shiga. Zaman tsit suke cikin motar chan da shirun ya masa yawa yace, “mesa bakisha ice cream naki ba? Bakiya son flavour’n ne?” “Inaso.” “Mesa bakisha ba toh?” “In muka dawo zansha in shaa Allah” ta amsa sa a takaice. Shiru ne ya sake ratsa su chan yace, “I miss your coffee” sincerely. Kuma hakan ne rabuwansa da coffeen ta he can’t even remember. “Muje office naka ko painthouse in had’a maka.” tace. Duk wannan magana da suke bata juyo ta kallesa ba shiko fuskarta yakeson kalla dan tayi kyau sosai, maroon jan bakin data sa ya mugun amsarta dukda kuwa fuskarta yad’an kumbura dan kukan data sha jiya dakuma yau da safe. “Fannah look at me.” Ya buk’ace ta ba musu ta juyo. Murmushi ya saki mata daga heart nasa, “kinyi kyau.” Murmushin ta mayar masa “thanks and you too.” “Nikam ai kullum ina yin kyau” ya gwada janta da surutu. “Yes Anas, kullum kanayin kyau.” ta fad’a tare da miyar da kallonta gare da windon. Daga yadda take maganar ya karanchi batason surutu. Be sake tuhumarta ba dan bayyason tak’ura mata, abinda ke damunta kad’ai ma ya isheta. Enterprise nasa suka nufa ya bud’e mata k’ofar dan neman magana ba rik’e hannunta yayi ba wannan karan. Hannun nasa ya zagaya a waist nata tsam ya matso ta jikinsa suna shaqan k’amshin turaren juna. Ko uffan batace masa ba, duk abinda zeyi yayi atleast sunada aure yanzu ba zunubi. Tun shigarsu cikin Enterprise d’in ake ta congratulating nasu. Bayan sun shiga office nasa ya zauna kan couch a yayinda ta ke had’a masa coffeen ba abinda yake banda binta da kallo, flask dam ta cika masa tare da sa masa cup ta kawo masa. Hannunta yaja ta zauna gefensa. “Thank you” yace da ita. Murmushi tamayar masa as a reply. Bayan ya kurb’e rabi yayi pausing. “Kefa zakisha?” Kai ta girgiza masa. “Why?” ya tambaya. “Toh ka tab’a min tayi neh?” Ta amsa tambayarsa da tambaya, abinda ya tsana kenan. “Da biyu kikayi hakan koh?” “Meneh?” Ta juyo tana kallonsa. “Again! Aswering my question with another question.” “I’m sorry Mr. Fauzi na manta rules naka ne.” Cup nasan ya mik’a mata da ragowar coffeen ciki. “Shanye lets go.” “Se wanda kasha zaka bani?” “Admit it Fannah kidena so kina kaiwa kasuwa, tunba yau ba kike kallona in ina shan coffee kinason sha daga cup d’ina. Na baki yau so kisha.” “Oh please Mr. Fauzi girman kanka yayi yawa wallahi, I pity duk wata macen dazata aureka.” “Kema haka I pity duk wani mijin da ze aureki, kisha lets go.” “Ni barin sha ba” ta fad’a stubbornly. “Okay shikenan tashi mukoma hotel namu toh, da rabon bakison ganin Mami.” “Haba! mana Anas me had’in shan coffee na da kaini gida gun Mami kuma?” “Nima bansani ba all I know is that sekinsha zan kaiki.” Harara ta watsa masa aiko yaganta. “Ni kike harara ko me ake kiran abun?” “A’a nifa ba harararka nake ba abu nagani agashin ka” ta masa qarya, nan tasa hannu cikin gashin nasa seyi take kamar tana cire abu. Chan taciro hannun nata. “Ina abun?” Ya tambayeta. “Na yasar.” Yasan sarai k’arya take kawai ya mata murmushi. Coffeen ta kurb’e tas ashe de da dad’i. Zata iya irga so nawa take shan coffeen befi sau uku ba dana yau kenan, gaskia she have been missing. Harshe taciro ta lashe lips nata. Kallonta yake in a cute manner. “Zaki k’ar” Sarai yasanta da ci zatace eh aikuwa ta gyad’a kai. “Toh baraki k’ara ba ai nawa ne tashi mutafi.” “Toh Anas I will make another one.” “Zaki b’ata min lokaci mutafi.” “Anas please.” “Fannah please lets go.” Haka Anas ya hanata shan coffeen. Ahmad yasa ya sauk’o masa da coffee machine da flask nasa ta yadda zata na had’a masa coffee always. Bayan isarsu gidansu Fannah ta ruga a guje tashiga da Mami ta soma cin karo hugging nata tayi har tana hanata nishi. Bayan sun zazzauna Mami ta kawo musu d’anwake me rai da lafiya yasha had’i kam. Bajewa Fannah tayi taci kamar ba gobe sekace wacce batayi breakfast ba kallonta kawai Anas yake ko tab’a nasa beyi ba saboda he is not a fan of d’an wake be iya ci ba, inma zeci sede ya tsotse zak’in kawai. “Baba na ya baka cin naka?” Mami ta tambayesa. “Bakomai Mami kawai ban iya chi bane, I'm sorry.” “Su Mr. Fauzi ajebo, gaba takaini” Fannah tace chan k’asa k’asa yadda Anas kad’ai dake kusa da ita ya jiyota. Ignoring nata kawai yayi. Plate nasan taja ta soma chi bayan data k’are nata. Afrah da Mami kam baki suka bud’e suna kallon ikon Allah. Cike da kunya Mami tace, “haba Fannah taya zaki d’au nasa kuma.” “Mami bakiji me yace bane? Cewa yayi baya ci, ajebo ne shi.” Cike da mamaki Mami ta bud’e baki zata masifeta. Da wuri Anas ya katse ta, “A’a Mami barta please, chi abin ki kinji?” Taci morethan half of plate nasa sannan tajita dam. “Mu tafi koh?” Ya tambayeta. “Mami zamu koma inason mu gaida su Ummie ma.” Kafin Mami tayi magana Fannah ta rigata. “Tafiya kuma Anas? Na d’au fa zaka ajiye ni ne kayi tafiyarka se anjima kadawo ka d’aukeni.” A ransa yace dake driver’n kine niba? A fili yace, “Fannah sweetheart kinsan zamuje mu gaishe dasu Ummie fah, ba time.” Ganin zasu fara muse-musen ma’aurta Mami tayi excusing kanta tare da jawo Afrah ma suka basu space. Ganin haka yace, “Driver’n kine ni ai da zaki sani jeka ka dawo, tashi mutafi, aikinga su Mamin.” Fuska ta maraice “ayyah amman banga Baba ba fa yana bacci. Yi hak’uri please kabarni in wuni anan wallahi chan ba dad’i.” “Ohonki tashi mutafi, ina ni kike cema ajebo kina zagina, stand up lets go.” “A’a I take that back dan Allah kayi hak’uri.” “Nak’i tashi mu tafi.” “Anas please” ta shakwab’e fuska tana murza ido. Yasan sarai zata iya fashe masa da kuka anan. Nanne mami ta fito daga d’akin. Ganin ta cika hawaye a idanunta yasa hannu tare da rik’o fuskar natan, “muga yafita?” Iska ya hura mata a idon “sannu ko?” Kai ta gyad’ “eh ya fita.” Chan k’asa k’asa tace, “ka yarda?” Harara ya galla mata tare da gyaran murya. “Uhm Mami zan tafi , zan bar Fannah anan I’ll be back in d’auketa.” “Toh toh yayi kyau sannu ko Baba na?” Dad’i sosai Fannah taji sebinsa da kallo take har yasa takalmansa. “Adawo lafiya baby.” Juyowa yayi tare da sakar da best smile nasa. “Thank you” sannan ya fice. “Soyayya ruwan zuma...” Cewar Afrah tana gyad’a kai. “Su wani baby kuka samu sara?” Banza da ita Fannah tayi seda Mami takoma d’aki bakin Fannah ya bud’u. “Amman ke mena cemiki? Bance karki samin english wears cikin akwatunan da zan tafi dasu ba?” “Toh meh? Ai naga da english wears ake amarchi” nan ta kewaya taga ba Mami “Ya Fannah ya first night d’in? Kinyi kuka?” “K’asaran ki maras kunya kawai nima bansani ba.” “Heheh!” ta sheqe da dariya, “Toh Allah kawo zuriah d’ayyiba yasa du sharpshooters ne” nan iphone nata yayi k’ara alaman shigowar message. Tana bud’ewa taga airtime ne na dubu biyu hot baby nata yamata sending. Bayan tayi replying nasa tace a fili “Allah bar min kai yau akwai flexing a instagram da kallon stories a snapchat.” Har yanzu Fannah ta kasa rufe baki a iya sanin ta de Iphone 5s ce wayar Afrah how comes take rik’e 6s plus yanzu? “Ke ina kika samu wannan k’aton wayar? Waya baki?” “Wanne wai?” ta tambaya cike da tsiya. “Awww Iphone d’ina? Hot baby ya siya min wallahi, yayi kyau ko?” “Hot baby wa kenan?” ta kuma tambaya cike da rashin fahimta. “Wa kuwa inba Shettima darling ba, business nasa se bunk’asa yake wallahi.” Dariya sosai Fannah ta sheqe da dan tasan ina yake samun kud’in daya ke kashe mata. “Shi business d’in kenan?” “Eh mana abin hassada ne kuma?” “A’a babyn Shettima Allah barku tare ni taho ki tayani in shirya atamfofina gu d’aya dasu zan koma.” Afrah ta bud’e baki zata kuma wani zancen Fannah ta katse ta “a’a banason bayani muje.” Suna hira suna shirya kayakin har suka gama. _11:30AM_ Daidai nan Anas ya dawo d’aukanta beso sake shiga ba se kawai ya kira ta ta waya alokacin wayar tata na d’akinsu itako tana d’akin Baba se hira suke bazawa kamar ance ta mik’e tace bari taje d’aki. Tana shiga taji rurin wayarta nan ta d’aga tare da duban waye. ‘Anas’ taga tubuce kai. K’in picking tayi dan battason sake komawa hotel nasun nan its so boring. Se a karo na biyu ta d’aga nanma seda ya kusa tsinkewa. “Kifito I’m waiting for you.” “Anas mana please, bamu had’u da Aiman bafa, tana school se 1:00AM zata dawo kaji? In jira?” “Banji ba kuma baraki jira ba, Fannah kifito don’t let me repeat myself.” Karap ya katse wayar, tsuka taja. Aiko ya fad’a kunnen Mami. “Keda waye ne?” “Erm.. Ermm...” kafin ta had’o k’arya Mami tace, “keda Anas ko? Fannah tun ba’ayi nisa ba kin soma masa rashin kunya, iyyeh? Me dalili?” “Mami waifa har ya dawo infito mu tafi.” ta fad’a tana turo baki. “Toh se meh? Out!” ta nuna mata k’ofa. Dake kafad’a tayi. “Fannah zan sab’a miki fa!” Haka kamar wacce zatayi kuka taja akwatinta ta fice ko sauraron Afrah batai ba. Bayan fitarta ta bud’e gidan baya tasa akwatin yana kallonta bece komai ba. Tana shiga ya kunna motar ba wanda yace ma wani ko uffan. Bayan isarsu gida suka gaggaisa, Ummie kamar ta cinye Fannah. Besamu ya had’u da Amal ba dake tana school haka Shettima ma. “Kuyi sauri ku gama gaisawan ku zan d’au abu cikin d’akina ne yanzu mukoma.” “Kai Babana daman ba yini kuka zo mana ba?” “Yini? A’a fa Ummie gaisuwan minti biyar ne kacal.” Yana kaiwa nan yashige d’akinsa. “Oh! Fannah kinga halin mijin naki ko? Yafiye rowa dayawa.” Murmushi cike da kunya ta saki tana kare fuskarta. Bayan shigan Anas d’akinsa ya nufa wajen safe dan ciro kud’ad’ensa wanda ze buk’ata to his suprise yaga an kwashe kusan rabin kud’ad’en. Dubawa dakyau ya kuma yi yaga eh fa kud’in nasa ne babu to waye ya masa wannan d’anyen aiki? Rufewa yayi tare da dawo wa cikin parlon “Ummie” ya kira sunanta. “Kin d’au abu cikin d’akina?” “Kamar ya abu kuma Anas?” “I mean my money morethan half of it are gone.” “Wai! Wai! Ka duba dakyau kuwa?” “Eh jeki duba kiga” nan ta mik’e ta nufa d’akin nasa. Ganin haka Fannah ta b’arke da dariya har rufe bakinta take, ashe nan ne business na Shettima yake bunk’asa tunda Anas bai gida. Kallon ta Anas yake ya rasa dalilin dariyar tata. Ummie tagama dube dubenta ba kud’ad’en, ko kad’an Anas be kawo aransa Shettima neba. ***** “Bari in yaran suka dawo zan tambayesu halan sunkai wani wajen daban.” Cewar Ummie dake tsaye bakin k’ofa ayayinda Anas ke k’ok’arin kunna mota. “Okay in Abuu ya dawo ki gaishe min shi.” “Toh, amaryar mu semun shigo ko? Mungode.” “Yawwa Ummie se anjima” Fannah ta amsata. Acikin motan ne Anas ya juyo yana kallon Fannah. “Dariyan me kuke d’azu?” “Da yaushe?” Ta tambaya pretending as if bata gano inda ya dosa ba. “Fannah banaso answer me.” “Babu kawai daga yin dariya yazama matsala.” “Bari zakiyi mafarki ma ai yau zamuga waze zauna dake, infact seperate d’aki ma zan kama.” Jin haka tace, “a’a zan fad’a maka.” “Good ina jinki.” “All I know is business na Shettima ya bunk’asa.” “Kamar ya kenan?” ya katse ta. “Oho nifa kar azo ace ina had’a munafirci.” “Just tell me.” “Promise barakayi reacting akai ba?” “I promise.” “Nide naga Afrah da 6s plus kuma tace Shettima ya siya mata.” “6s plus?” Ya tambaya tare da juyowa yana kallon ta cike da mamaki. “Anas kalli gabanka please kar ka bugamu ko mu fad’a rami.” “Wato da kud'i na aka sai wa Afrah 6s plus d’in koh? Da kud’in mijinki shine kike dariya. Da kyau zamu had’u dashi.” “Toh me zanyi? Shida kud’in yayansa. Plus a’a Mr. Fauzi kaga you promised you won’t react.” “So kike inyi shiru in zuba masa ido? Ya kwashe morethan half of kud’in dake cikin safe d’ina fa.” “Hak’uri zakayi he is in love kuma dan baida aikinyi ne, let them be please, kaji Mr. Fauzi.” “You really wants to annoy me ko Miss Aleeyu?” “A’a Anas toh, nide kar ka masa magana.” Chan k’asa k’asa yace, “barin masa magana ba kamar yadda barin canza masa motar sa ba kuwa” “Yafi amman dekam karka masa magana.” tache. *© miemiebee* [12:56, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 5⃣9⃣ Chicken chop ya wuce dasu dan siyo musu roasted chicken. Bayan yayi parking yafito ya bud’e mata k’ofarta, kamar d’azu haka ya matso ta jikinsa. “Anas yanzu kama hannun ma kadena? Se haka?” Ta tambaya a nitse. “Eh na dena nan gaba ma I think d’aukan ki zan soma.” Bata sake che dashi k’ala ba suka shiga ciki d’aya daga cikin kujerun ya ja mata bayan ta zauna ya nufa wajen siyan. Shiru Fannah ta zauna tana ‘yan kalle-kalle kafin ta hankara ta jiyo sallamar sabon murya akanta. Data d’ago kai taga matashi ne jik’a a jini ko suyi shekaru d’aya da Anas koya girmi Anas da kad’an. “Wa’alaikumus-salam” ta amsa sa d’auke da murmushi a fuskarta. “May I sit?” ya buk’ata in a calm way. “Yes sure.” Nan yaja kujerar dake kusa da ita ya zauna. “Koban tambaya bama nasan bakida aure ko?” Murmushi ta saki tare da girgiza kai ta bud’e baki zatayi magana kawai taga Anas from nowhere ya cukumo kolar rigar bawan Allah yakai masa punch a fuska take gefen bakinsa ya fashe. A firgice ta mik’e “Ya Salam! Anas meh hakan please? Taya zaka hau dukansa be maka komai ba, ka sake shi.” “Bemin komai ba? Are you kidding me Fannah?” hannun mutumin ya murd’a ta bayansa cike da mugunta wanda har yasa mutumin sakar da k’ara. Cike da azaba yace, “hey who are you? And meh na maka? Let me go will you? Taya zakazo ka kamani in public kana murd’a min hannu.” “Awww tambaya ma kake meka min?” “Anas everybody is starring at us dan Allah ka sake shi, its embarrassing” Fannah ta katsesa cikin salon da bareji haushi ba. Juyawa yayi ya kalli jami’un wajen. “Mind your own god damn businesses! Now!” yace dasu a tsawace nan kowa yacigba da harkan gabansa. “Barin maka warning, ko a lahira kaga Fannah karkayi yunk’urin mata magana ‘cause it might be the end of you, ba’a mutuwa a lahira but when it comes to toasting my wife I could kill you. Do you get me?” Ya sake murd’a wa mutumin hannu. Cike da azaba da mamaki mutumin ya d’ago kai yana kallon Fannah data tsure itama. “Why didn’t you tell me you were married?” Abinda yace kenan. Wani irin gulity concious ne ya kama Fannah. “You mean you didn’t know?” Anas ya tambaya cike da mamaki shima. “Bawan Allah a tunaninka haka kawai zan hau toasting mace me aure ne? Seda na tambayeta ko matar aure ce ita sekuma ta min shiru. Da shigowa na garin nan sati kenan I know barely no one.” Take Anas ya sake sa “I’m so sorry please kaji? Accept my apologies.” Seda mutumin ya k’are masa kallo sannan yace, “accepted amman nan gaba don’t just jump into conclussion” yana kaiwa nan ya waiwayo ya kalli Fannah tare da kad’a kai sannan ya fice. Hannunta Anas ya finciko cike da azaba ita kanta tasan she is in trouble ko d’ago kai taga ya yanayin fuskarsa take ma batai ba a iya sanin ta fuskarsa da idanunsa zasu iya fin jan kala yin ja saboda daga yadda yake nishi za’a iya kwatanta b’acin ransa. K’ara ta saki tana k’ok’ari k’watan hannun nata. Bakin k’ofa yajata. “Sir your order is ready” ko jin mutumin beyi ba yajata suka fice daidai motarsa yayi wulli da ita kad’an ya rage bata fad’i ba. “Get in” yace cike da b’acin rai hawaye tasoma wanda batasan lokacin ba, a hankali ta bud’e k’ofar ta shiga ya kunna mota. Koda suka isa hotel d’in fitowa yayi tsaye yana jirarta bayan tafito yakuma kama hannunta irin na d’azu. “Anas dan Allah ka saken da zafi.” Ko sauraronta beyi ba ahaka har suka haura d’akinsu. Banging k’ofar yayi da k’arfi tare da bugata jikin k’ofar. Ba abinda take banda kuka ba sauti dakuma b’ari. Dududu ratan dake tsakanin fuskarsa da nata befi inchi biyu zuwa uku ba. Wani irin kallo yake mata tsabagen yadda ransa ya b’aci yama rasa me ze mata. Cikin wani irin tsawacaccen murya yace, “bakida hankali neh?! Kina matar aure zaki zauna kusa da wani? For crying out loud harda k’in cemasa you are a married woman? Huh?!” Kai kawai take girgiza masa hawaye nabin k’uncinta. “I’m talking you!” ya fad’a a tsawace tare da sake buga jikin k’ofar. B’ari take harwani sama sama nishinta yake, “Anas dan Allah kayi hak’uri, I’m sorry please.” “You still haven’t answered my question. Why Fannah? Answer me!” Cikin sautin kuka tace, “Anas kaifa da bakinka ka fad’amin koda anyi bikin you can see any girl you want tunda contract marriage ne shine nima naga ai bawani abu ciki dan mutumin d’azu yamin magana.” “Damn it!” Ya sake buga k’ofar. “Damn everything Fannah! What if na fad’a miki I don’t mean it, tunda akayi bikin kinga naje gun wata ko wata tazo min ne? I don’t mean any of those words kawai na fad’a ne.” Ya k’are maganar yana kallon k’asa. “Anas I’m sorry dan Allah kayi hak’uri.” “No Fannah ke kanki kinsan what you did was wrong, how could you not respect our marriage?” Yana kaiwa nan ya juya binsa tayi, tayi hugging nasa ta baya tana meh hanasa koda motsi. “Anas I’m sorry dan Allah kayi hak’uri I thought you meant what you said shiyasa, am sorry please.” Har a yanzu baijin he can forgive her. Hannunsa yasa ya raba jikinsa da nata. “Anas please...” Ta rok’esa se ambaliya hawaye ke a fuskarta. Kayan jikinsa ya rage yabar shorts da vest zalla tare da hayewa kan couch ya kwanta. Kuka take har yanzu ba sauti ganin ba mahalicci se Allah ta mik’e ta nufa bayi, fuskarta ta wanke sannan tafito ta juye masa coffeen sa cikin cup tare da kai masa. Ganin haka ya juya mata baya. “Anas kayi hak’uri kasha please.” Banza da ita yayi. “Anas please, I said I’m sorry be isa ba?” Nanma banza da itan yayi. “Anas koda contract marriage ne tsakanin mu you are still my husband kadena fushi dani banasan tsinuwan mala’ikun rahma please talk to me.” Nanne yayi magana. “Ince miki meh?” “Anas me zan maka ka yafemin please, stop being mad.” Juyowa yayi yana kallon yadda take ta zubda hawaye sekuma ta basa tausayi. Coffeen ya amsa ya kurb’e tare da miyar mata da cup d’in. “Nasha shikenan?” “Anas bakace ka hak’ura ba.” Shiru yayi tamkar bejita ba. “Anas mana...” “Naji, bacci nakeji yanzu allow me, will you?” “To katashi ka haura gadon ka kwanta, kaji?” Shiru bece komai ba. Hannu tasa ta jijjik’a sa bece da ita komai ya mik’e ya nufa gadon ya kwanta. Mayafinta ta d’auka tayi bakin k’ofa. “Ina zakije?” Ya tambayeta. “Akwatina zan d’auko.” “Wait.” Nan ya d’au wayarsa yakira wani in less than 2 minutes aka kawo mata jakar tata. Amsa tayi ta bud’e ta soma jera wanda takeso da wanda battaso tun Anas yana kallonta har yayi bacci. Bayan ta gama taga still da saura Azahar. Kan couch d’in ta nufa ta mik’e nan itama tayi baccin. ***** Sakamakon ihun da Anas ya tsala ne ya farkar da ita daga bacci a firgice. Ganinsa tayi zaune kan gadon ya had’a wani irin gumi da sauri ta nufesa. “Anas” ta kira sunansa, beko amsata ba se girgiza kai dayake. Remote na AC ta d’aga ta k’ara k’arfin. “Anas are you okay?” Ta tambaya a nitse. Nan ma be amsata ba. Tissue ta zaro tana goge masa gumin nasa bayan data gama ta yasar sannan ta dawo ta zauna kusa dashi. Hannunsa ta d’aga tayi interwining yatunsu su a hankali. “Anas mafarki kayi?” Kai ya gyad’a mata. “Want to talk about it?” Kai ya girgiza. “Okay toh keep calm kaji, I’m here if you need someone.” Chan k’asa k’asa yache, “yarinyan ta dawo.” “Yarinya kuma?” Ta tambaya cike da rashin fahimta. “Wace yarinya kenan Anas?” “Yarinya from the incident. *_TANA TARE DA NI..._* haka tacemin kuma nima I can feel it. *_TANA TARE DA NI..._* Ina take?” Ya d’ago idanunsa da basu gama dawowa asalin colournsu ba yana kallonta. “Anas bansan wace yarinya kake magana ba, its just a dream kaji? Inma wata yarinyar kake nema sooner or later zata bayyana maka, kaji?” Kai ya gyad’a tare da mik’ewa kan gadon, kansa ya aza akan cinyoyinta masu uban laushi da tsoka daidai ya kwanta. Bata ce masa komai ba ya daidaita position na kansa akanta yana kallon d’ayan direction d’in. Fannah kad’ai tasan irin electric sparks da suke going mata ajiki. Wannan ne karo na farko dawani d’a na miji ke kwanciya mata a cinya. “Fannah kina ganin zata yafemin abinda na mata?” Yace da ita cikin wani irin salo. Shiru tayi danko batasan ina ya dosa ba. “Wa ce kenan?” Ta tambaya. “Yarinyar, kina ganin she can forgive me despite abinda na mata?” “Me kama ta Anas?” ta tambaya cike da neman k’arin bayani. “Its horrible I can’t say it, na cuce ta nasani shiyasa koda in mun had’u tace sena aureta zata yafemin zan aureta, I will do it” Bugun zuciyarta taji ya k’aru, meh Anas yana wannan yarinyar dayake fad’in ze aure ta na hak’ik’a? Shida bayason aure koda wasa yake cewa zeyi toh mesa? Kamarya ya cuce ta kuma? Toh kode ciki ya mata ya gudu? kai a’a Anas beyi kalan me bin mata ba har ace yama wata ciki, toh me ya mata? Shi ya tsamota daga duniyar tunanin data wula. “Fannah kinaga zata yafemin in na bata labari na?” Hannu tasa cikin silky gashin kansa me uban tsayi da cika daidai ba kamar nata ba. Shafa gashin nasa take a hankali tana curling wasu a yatsunta. “I’m sure zata yafe maka Anas muddin kayi nadaman koma mene ka mata, dakuma in ta sake jin labarinka. Zata yafe maka kaji?” Kai ya gyad’a a hankali. Daga nan be sake cewa komai ba. Bayan like 10 minutes takira sunansa shiru taji be amsa ba. Data lek’a fuskarsa setaga har yayi bacci no wonder taji ya k’ara nauyi. Dukda cewar idanun sa a rufe suke se ji take a jikinta ta tab’a sanin Anas a wani gun to a ina ne? Hannu tasa ta rufe fuskarsa tabar daidai wajen idanun nasa, nan kamannin nasa ya sake fito mata sede ta rasa gane a ina ta sansa. Maybe me kama dashi na sani ai wannan girman London yayi nikuma ban tab’a zuwa chan ba, theres no way zamu tab’a had’uwa. Ta tunatar da kanta a zuci. D’an k’ara ta sakar sakamakon zogin da cinyarta na dama ke mata ta inda kan Anas yafi nauyi. “Anas” ta sake kiran sunansa. “Uhmmm” yayi groaning cikin sautin bacci. “Anas ka koma kan pillow naka kaji? Cinya na ya soma yin tsami.” Shiru yayi dan bema jita ba daidai kunnensa ta matso “Anas” ta kira sunansa. “Fannah let me sleep mana kinji?” “Toh Anas cinya na zafi.” “Please...” Badan tanaso ba ta amince. Gashin kansa take ta wasa dashi har gwada kitsawa take sede da ya kitsu se ya warware dan santsi ba kamar ta ta me uban tauri ba gara ma ace in tayi stretching. Chan cinyar hagunta ma yasoma ciwo. Hak’ura kawai tayi batasan seda ta fara gyangyad’i ba da taji zata fad’i seta farka ai haka bacci b’arawo yasata gaba batasan lokacinda ta fad’a kan Anas ba, kayinta kan nasa a yayinda nasa ke kan cinyarta. Bacci sosai duka sukeyi cikin kwanciyar hankali. ****** Se 2:30PM Anas ya tashi ko Sallah basuyi ba. Ji yayi nishin mutum a kansa gakuma alamun gashi kan fuskarsa wanda yanada tabbacin ba nasa bane. Hannu yasa yana tattab’ata har ya gano mace ce a kansa kuma Fannah ce. How comes? Ya tambayi kansa, nan ya tuna duk wani abinda ya faru. Gosh no! Why do I have to tell her? What if ta gane na tab’a raping wata a rayuwa na? God help me. Duk wannan magana da yake a zuci yayi su. “Fannah” ya kira sunanta. Bacci take har yanzu bata ko motsa ba, “Fannah” yasake kira yana jijjiqa ta danko motsawa ya kasa duk nauyin ta na akansa. “Fannah wake up” nanne ta d’an bud’e ido. “Wake up kinji? Bamuyi Sallah ba.” Firgit ta tashi daga kansa tana sosa ido ita kanta batasan ya akayi ta fad’a jikinsa tana bacci ba. “I’m sorry” tace masa. “I too” ya miyar mata. “You are sorry?” ta tambayesa cike da mamaki “for what?” “For ealier, for making you cry.” Dad’i taji iya dad’i atleast koda be fito fili yayi spelling mata SORRY ba ya kwatanta. “You are no more mad at me?” “Yes I’m not, also nagode.” “For...?” Ta tambayesa. “For letting me sleep on your laps.” “Ohh! bakomai you had a dream.” Shiru yayi kamar be jita ba dan bayyason ta tono da maganar. “Muyi Sallah first lokaci ya wuce.” Tsam ya mik’e ya nufa bayi ko motsawa Fannah batayi ba as se mik’a take. Bayan yafito yace, “you are next” tare da jawo wata bak’ar jallabiyansa yasa. Ai tana gwada mik’ewa tasaki wani irin wahalallen k’ara cike da azaba da sauri ya nufo inda take. “Fannah whats wrong?” Take idanunta suka cike da hawaye. “Meneh?” Cinyarta kawai take nuna masa se yanzu ya tuna time da take ce masa cinyarta yayi tsami yak’i tashi, seyaji guilty gabad’ai. “Dan kwanciyan danayi akai ne koh?” Ya tambayeta cikin wani irin salo cike da tausayi. Hawayen nata yasa hannu ya share mata. “Don’t worry zafin ba sosai bane just help me in mik’e.” Da ya gwada mik’ar da ita seta saki k’ara, tausayinta sosai yaji ya kama sa musamman ma ya tuna shine sanadi, besan lokacinda bakinsa suka furta *“I AM SORRY”* ba. Words data juma tana jiran ranan da ze furta mata su se gashi yau yayi. “Anas karka damu I’ll be fine.” “Taya barin damu ba bayan nine sanadi.” Da k’yar ya iya mik’ar da ita ya takata har zuwa bathroom d’in sannan yafito bayan data gama abinda zatayi ta kirasa yazo ya taimaka mata ya fito da ita tayi tayi ta fito da kanta amman takasa, ko yatsa ya tab’a cinyoyin nata zafi suke mata. Anas yayi tabari ya d’aga ta tak’i wai abin kunya ne taya da girman ta ze d’aga ta. Bayan ya tada Iqama ya juyo yana kallonta, yadda take ta yamutsa fuska cike da azaba. “Zaki iya yin Sallar a tsaye?” “Eh don’t worry, lets pray.” Har hawaye seda ta zubar acikin sallar musamman suka zoyin sujjada da zaman tahiya. Bayan da suka idar ya juyo yana kallonta nan ya karanchi tayi kuka. Cikin akwatinsa ya nufa ya zaro wani man muscle pain killer ya nufo inda take. Kallonsa take cike da rashin fahimta. K’afanta d’aya yaja a hankali a yayinda ta sakar dawani irin k’ara dan azaba. “Sorry” yace da ita. Ganin yana k’ok’arin kwaye mata abaya tasa hannu ta rik’e nasa. “Anas lafiya me haka?” “Fannah magani zan shafa miki.” “A cinyan?” ta tambayesa tana zaro ido waje cike da mamaki. “Eh” ya bata takaicaccen amsa. “A’a’ahhh!” ta sake baki tana kallonsa. Taya ze gane mata cinya ana zaman lafiya ai ta gwammaci tacigaba da zama da cinyar haka har seda ze sab’e da kansa. Kayan nata ta matse gam a jikinta. “Fannah me haka?” “Banaso, kabari ze warke da kansa.” “Kinga banson sututan banza yaushe nene ze warken? Harfa kuka kikayi da muke Sallah, bari na shafa miki.” “Anas banaso please ka bari.” “Dalili?” “Dalili kuwa itace taya zan kwaye maka cinya na a waje? Gaskia ba kyau kabari kawai.” “Toh ba mijin ki ne niba? Naga dama ko ba kaya ajikinki zan kalleki amman I’m not interested, cinyarkin ma dan yazamo dole ne. Bring it.” Kafad’a ta buga “o’o gaskia ni banaso.” “Fannah kinason in miki na k’arfi koh? Ki kawo k’afar, mema zan gani ajikinki wanda bangani ba a waje.” “Eh ni koma me banaso, kaje kata ganin na karuwai a waje amman banda nawa.” “Haka kikace?” “Eh mana taya ana zaman lafiya zan hau kwaye maka cinya na.” “Okay you want it in a trouble way, you are gonna get it.” Ajiye maganin yayi gefe guda ya rik’o siraran hannayenta biyu cikin nasa guda d’aya... *© miemiebee* [12:56, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 6⃣ 0⃣ “Anas wai me haka? Kasake min hannu.” Se k’ok’arin k’watan hannun nata take amman takasa. “Barin sake ba, is better kibar wannan fad’an da kikeyi ‘cause sena shafa miki zan bar nan.” “Anas dan Allah kayi hak’uri zan shafa da kaina, kaji?” “Banji ba” kayan nata yasoma yunk’urin kwayewa, wani ihu ta sakar seda ya tsaya yana toshe kunne. “Me haka? Fyad’e zan miki? Ko yanka ki zanyi?” Kai take girgiza masa, “a’a Anas dan Allah ka sakemin hannu banaso please dan Allah.” “Amiki a sanyi kink’i ba, barin sake miki hannun ba.” k’afafun nata ta gwada shurewa aiko cinyar tata suka soma zafi. “Wayyo Allah! Cinya na!” “Ai kad’an kika gani, I told you to stop fighting it kink’i.” Kayan nata ya kwaye zuwa guiwarta. “Anas dan Allah kabari ba kyau wallahi haramun ne karka kwaye min kaya please.” bata bar k’ok’arin k’watan hannun nata ba har yanzu sede sam ta kasa dan ko rawa hannun Anas baiyi. Beko saurareta ba ya d’aga kayan nata sama, harta panties nata seda ya bayyana, santala santalan fararen cinyoyinta masu gashi dogaye kwance akai suma suka bayyano. Ganin haka ta fashe masa da kuka “Anas dan Allah kabari ka rufe min cinya bakyau wallahi.” “Gomma ma kiyi shiru dan ba sauraranki zanba.” Maganin ya bud’e da d’ayan hannunsa ya matse kan cinyartan duk da hannu d’aya. Yana gwada murzawa ta saki wani irin k’aran da sekace ana cire mata rai, da ace akwai mutane kusa dasu da se sun fiffito. “Wayyo Anas dan Allah kayi hak’uri in kanayi wa Allah karka sake tab’amin cinya wallahi da zafi, kayi hak’uri dan Allah” ta kuma fashewa da kuka. “Fannah inba’a murza ba bare wassake ba k’afan naki tsami zeyi.” “Na yarda wallahi amman dan Allah karka sake tab’awa da zafi sosai.” Kuka take harda majina. “Fannah I’m sorry bareyi inbar ki haka ba, just close your eyes kinji?” “Anas dan Allah karka sa-” ihu ta sakar sanadin murza maganin kan cinyarta dayayi da k’arfi. “Arghhhh! Wayyo Allah na mutu.” Murza man yake sosai kan cinyarta da k’arfi in bahaka ba tsami zeyi. Sosai Fannah take kuka fuskar nan duk hawaye da majina seda ya tabbata yashafa mata man zafin kota ina a cinyan ya sake mata hannu ta huta kafin ya shafa a d’ayan. Bata bar kukan ba har yanzu, hannunta har yayi shati dan yadda Anas ya rik’eta, kayan nata ta mayar a wahalance ta rufe jikinta dashi. Ruwa ya tsiyayo mata daga dispenser tare da d’ibo tissue. Nishinta har wani sama sama yake dan kuka. “Fannah ya isa mana” fuskarta ya rik’o ta fisge da wuri. Murmushi kad’an ya saki “yi hak’uri toh. Kawo face naki na miki clearing.” “Banaso zanyi da kaina.” “A’a ni zan miki.” “Nikuma banaso haka kawai dan kaga kafi k’arfina seka na min mugunta.” Fuskar nata ya sake rik’owa “don’t fight it Fannah ki tsaya.” Badan tanaso ba tasaida fuskar natan hancinta ya goge mata sannan ya share mata hawayen. “Ga ruwa sha kinji?” “Banaso.” “Yi hak’uri kisha kinji?” ya d’ago cup d’in tare da kai mata baki. K’in bud’e bakin tayi. “Fannah kisha or else in sake matsa miki k’afan” jin haka ta bud’e bakin nata tasha kusan rabi. “Good sauran d’ayan koh?” “A’a wallahi d’ayan baya ciwo.” Tsbagen yadda ta tsure bata ma san seda ta rantse akan k’arya ba. “Naji baya yi tsaya mu shafa miki shima.” Sabon kuka ta soma “Anas kayi hak’uri dan Allah” jikinsa take turewa daga gareta. “Fannah kinga ki tsaya mushafa miki a hankali ko kalan na d’azu kikeso?” “A’a banason ko d’aya.” Kayan nata ya soma kwayewa a yayinda take taresa, “dan Allah karka min haka please.” Be saurara mata ba ya had’a hannayenta biyu gu d’aya cikin nasa. “Anas wallahi zan cije ka in baka sakeni ba.” “Don’t worry ko kin cijen barin bari ba” nan ya sake kwaye mata kayan, ganin yasa man zafin kan cinyarta ta tsala ihu, ignoring nata yayi ya soma murzawa da zafi zafi se ihu se kuka take, daga k’arshe ma seizing muryar tata tayi se hawaye kawai take zubarwa. Bayan daya gama ya share mata hanci da fuska sekuka take har a yanzu. D’agota yayi chak kamar ‘yar baby ya aza ta kan gado ganin batada niyan barin kukan yayi joining nata akan gadon shima tare da kwantar da kanta akan k’irjinsa yana bubbuga bayanta a hankali. “Shhh! ya isa kinji? Bar kuka.” “Allah ze sak’amin” tace cikin sautin kuka. “Eh ze sak’a miki bar kukan amma.” Se chan datayi shiru ya tambayeta, “are you hungry?” Kai ta gyad’a masa nan ya miyar da kanta kan pillow yayi musu ordering abinci. Bayan abincin ya iso ya buk’ace ta da ta sauk’o da k’yar take taka k’afar bayan sun gama chi ta mik’e da tafiyar tata d’ai d’ai, towel nata ta ja da hijabi ta shiga bayi ruwa ta watsa sannan ta fito, kamar yadda ta saba cikin hijabi take sa kaya, wata red simple doguwar riga tasa ta haye gado ta kwanta. **** _9:30PM_ Yanzu suke gama cin dinner, inbanda bin Fannah da kallo ba abinda Anas yake, bayan tagama duk wani abinda zatayi ta haura gado ta kwanta se anan ya d’auko maganin zafin tare da hayewa gadon shima. “Oya mik’o k’afan ashafa miki.” “Wallahi barin yarda ba, ai yazama mugunta kenan, ka shafa min d’azu ai ya isa.” “In miki kalan na d’azu kenan.” “Ai wando ne a jikina ba yadda zaka ciremin kuma.” Murmushi ya saki ta gefen da dimple nasa yake. “Haka kikace?” Kai ta gyad’a masa. “Okay” kawai yace mata tare da jawo ta da hannu d’aya seda ta fad’a jikinsa. “Anas me haka? Ka sakeni bacci nakeji.” D’ayan hannun nata ya sake ja tare da had’asu waje d’aya da d’ayan hannunsa ya soma sauk’e mata wandon baccin nata. “Anas dan Allah kayi hak’uri wallahi ba kyau kadena dan Allah. Wallahi iskanci ba kyau.” “Ba cewa kikayi barin iyaba? we shall see.” “A’a zaka iya, wallahi zaka iya kayi hak’uri dan Allah karka ciremin dan Allah.” Ko saurara mata beyi ba seda ya sauk’o da wandon nata har guiwa light pink pant nata ya bayyana. Haka yabi duka cinyoyin nata yashafa mata man zafin. Ba irin had’asa da Allan da batayi ba. Bayan daya gama ya sake mayar mata da wandonta sannan ya sake mata hannu. “Wallahi Allah ze sak’a min.” “Toh me zan kalla a jikinki Fannah? Light pink panties naki ko meh?” Pillow taja ta rufe fuskarta dan kunya she still can’t believe Anas yagane mata pant. Bada dad’ewa ba shima ya haye gadon ya kwanta. “Fannah” ya kira sunata. Batayi bacci ba amman tak’i amsa sa. Pillonsa ya matso kusa da nata nan tayi baya da nata haka suka tayi seda ta isa k’arshen gadon rukuna. “Wai Anas me haka?” Shiru ya mata bece komai ba. Chan itama tayi baccin bata jima da farawa ba ta fara mafarke mafarkenta sede na yau beyi nisa ba ta tashi da wuri. Tsoro ta soma ji hannunta ta had’a da nasa ta matse gagam, ganin bata dena jin tsoron ba tabar kan pillonta ta kwanta akan k’irjinsa tare da zagaye hannunta kan cikinsa nanne tasamu tayi baccin itama. Sab’anin kullum Anas ne ya fara tashi yau, ganin Fannah yayi kwance a jikinsa se baccinta take sha koda ya gwada d’age hannunta daga kan cikinsa gangamesa ta sake, da k’yar yasamu ya raba jikin sa da nata. Suna zaune bayan sun idar da Sallan Asuba sungama Azkhar kenan Anas yace, “ya k’afan naki?” “Da sauki ya warke.” “Aikoda ya warke se na sake shafa miki anjima.” “Wallahi Anas ya warke kayi hak’uri.” “Yau bakiyi mafarki ba.” “Eh...” Ta amsa shiru. “Kodan saboda kwanciya da kikayi ajikina?” Bata masa k’arya ba tace “eh, kaima ai da kayi mafarkin yarinyar chan seda ka kwanta kan cinya na.” Shiru yayi kamar be jita ba dan bayason maganan yarinyar. “Anas wace yarinyar?” “Kinga irin suratan ki d’inba? Ke waye mutumin? I'm going back to sleep.” A rarrabe suka kwanta. _10:40AM_ “Anas kayi hak’uri ka kaini Saloon d’in mana.” “Barin kai ba ina ni kike cema mugu.” “Nikuma da yaushe?” “D’azu da nake shafa miki muscle pain reliever.” “I’m sorry zafi ne yamin yawa.” “Shine zakije saloon da k’afar nakin?” “Toh Anas nagaji da zama dakan a tsefe haka, ko calaba ne zasumin it won’t take long.” “In calaba ne ai nima na iya.” “Ka iya kitso?” Ta tambaya tana zaro ido. “Ba kitso nace miki na iya ba, calaba na iya, inayi wa Amal.” “Toh ai ni ba Amal ceba ka kaini saloon d’in please.” “No Fannah barakije ba, naga har maza ake ajiye wa a saloon na mata yanzu barakije wani gardi yaga gashin kiba.” “Toh Anas sekace nikad’ai ce mace a wajen? Ai hak’uri zakayi.” “Barin iya ba nemo comb na miki calaban.” A zuciyarta tace ai kuma wallahi seka kitsa. Nan ta d’au comb cikin jakarta ta kawo masa yana zaune kan gado. “Gashi” ta mik’a masa, amsa yayi tare da mik’ewa. Gaban dressing mirror ya jata ya zaunar da ita kan kujerar. Ribbon nata ya warware seda yaji tsoro dan yadda gashin yayi wani buf! “Ke wani irin gashi ne haka? Dama haka gashin naki yake? Barin iya ba miyar da ribbon nakin.” “Haba mana Anas sekace yau ka fara gani, to ka kaini saloon d’in tunda baraka iya ba.” “Nifa na fad’a miki bara kije ba.” Gashin nata ya taje sama sama sannan ya tsaga ya soma kitsa mata calabar daga ta k’eya. “Awcchh! Anas da zafi kad’an rage zafin hannun naka mana.” “Kinga fa banason fitina ko ki zauna ko in fasa, kinma samu zan kitsa miki kai kina min tsiya.” “Toh yi hak’uri amman kad’an rage zafin hannun please.” Sun d’au kusan minti biyar be gama kitsa ko d’aya ba, har Fannah tagaji da zama. “Anas har yanzu bamu gama ko d’aya ba?” “Acewarki kitsa wannan uban gashinkin is easy neh? Ni barin na k’arasawa har bakin ba yayi tsawo dayawa.” “Amman Anas ai ze warware, yi hak’uri ka k’arasa.” Cikin awa d’aya guda biyar kacal sukayi. “Nagaji se anjima.” “Anas biyar kacal fa mukayi.” “Ina sane ai, in kinaso mu gama a yau muyi trimming bakin gashin seya dawo d’aya dana Amal kinga then zan iya kitsa miki.” “Toh ai ba kyau Anas.” “Naji Malama ke dama komai ba kyau” ribbon nata ya nema ya kama mata gashin. “In na huta zamu cigaba.” Hannunsa ta rik’o “Anas please kowani biyar d’in ka k’ara seka huta gaji? Yi hak’uri.” “Fannah kalli nan” ya ciro hannunsa dake nan sekace bana miji ba dan laushi. “Kiga yadda gashin ki ya yanke min hannu.” “Yi hak’uri kaji zan maka tausa, please ko biyar ka k’ara.” Biyar d’in kuwa ya k’ara yace ze huta. Haka har dare yayi basu gama ba rabi sukayi sauran rabi. Se a washegari suka gama kitson, sosai kuwa k’ananun calaban daya matan yayi kyau sosai sekace wani k’wararre. “Wow! thank you yayi kyau.” ta fad’a a lokacin datake kallon kitson nata a madubi. “I know ba sekin fad’a ba.” “Kai Mr. Fauzi kullum cikun girman kai, in aka yaba abin da mutum yayi cewa yake thanks.” “Aww in miki kitso kuma in sake miki godiya? Lallai fah, kema girman kan Mr. Fauzi ya soma tab’aki Mrs. Fauzi.” ★‡★‡★‡ Da bikin Mr. Fauzi and Mrs Fauzi sati biyu kenan yau, sosai sun sake sabawa da juna sede kunsan halin Mr. Fauzi in abin nasa ya bugesa suburbud’awa Fannah rashin mutunci yake iya san ransa baiwar Allah kam sede ta zauna tayi kuka, inya tashi nuna mata care kuwa kamar ba gobe. Sauran sati uku agama masa gininsa su tare. Tun a daren jiya Sunday Fannah takejin alaman zuwan period nata ta duba kayakinta tasa ba pad ko d’aya ciki ta rasa wani irin shirya kaya Afrah ta mata dayasa ta mance da important abu haka ba. Gashi sunyi fad’a da Anas basu magana bale ta tambayesa kud’i taje ta siya. Kasancewar yau Monday, leave da Anas ya karb’a ya k’are yau zeyi resuming office. Kwance suke kan gado Fannah nachan nata b’angaren shima haka, Allah ma ya sota batai mafarki ba yau data shiga uku. Tun kafin Asubah ta tashi tana rik’e da k’asar mararta dan azaba, batasan lokacinda ta soma kuka ba. Sautin kukanta ya tada Anas dukda fad’a sukayi amman ganin ta tana kuka yaji tausayinta ya ratsa sa, duk yadda yayi dan ignoring nata ya kasa. Wutan d’akin ya kunna, tare da dafe bayanta “Fannah what is it? Mesa kike kuka?” Shiru ta masa har yanzu haushinsa takeji inta tuna yadda yata mata masifa jiya dan kawai ta gyara masa wardrobe nasa ko me yake b’oyewa ciki se Allah. Shiru ta masa bata amsa ba se k’ananun kukanta take. “Okay Fannah I’m sorry about yestarday kinji? Barin k’ara ba. Meke damunki?” Kamar wacce baratayi magana ba tace “Anas marata ciwo.” “Sorry ina zuwa” cikin kayansa ya shiga ya ciro pain killer da ruwa ya mik’a mata “gashi sha kinji? Sannu.” Amsa tayi ta had’iye har yanzu ciwon be dena ba. “Kwanta” ya buk’ace ta. “Barin iya ba Anas barni ahakan kawai.” “Fannah ki mik’e nace.” Nan ta kwanta juyo da ita yayi ta yadda tana kallon ceiling. Hannunsa ya aza kan cikinta daidai gun marar tata yana massaging. Hannunsa ta d’aga daga kan cikinta, “Anas meh haka? Ni banaso.” “Why do you always think negative? Niba abinda zan miki am just helping you.” “Toh shine seka tab’a min ciki?” “Fannah stop it” hannun nasa ya cire daga nata yacigaba da mata tausar. Sanyi taji sosai, har taji ciwon na raguwa haka yayi ta mata. Asuba nayi Anas ya shiga bathroom yayi alwala nanne Fannah taji sauk’an period nata. Anzo wajen tace a ranta. Batasan ta ya zata fara sanar da Anas batada pad ba duk yadda tayi barata iya ba kunya bare barta ba. “Anas I need money please kabani d’ari biyar.” “Me zakiyi dashi?” “Abu zan saya.” “Wani abu ne haka zaki siya da Asubah? Ko Sallah fa bamuyi ba.” Kawar da kanta tayi daga garesa, “banayi.” Tace chan k’asa k’asa. Sam be jitaba “tashi kiyi alwala muyi Sallah.” Kai ta girgiza masa. “Dan ciwon cikin ne barakiyi Sallah ba?” “A’a... Kawai kayi zanyi anjima.” “Kefa kikace Sallan jam’i yafi lada.” “Nasani kawai kayi naka yau d’in.” “Nak’i tashi kiyi alwala muyi Sallah kinsan inada office yau.” “Banayi” tace chan k’asa k’asa tare da kare fuskarta. “Shine baki fad’amin ba tun d’azu kika tasani surutu. Mschw!” Yaja k’aramin tsuka “kinada case wallahi.” Bayan ya idda Sallan ya hauro gadon ya kwanta. “Anas kaji kabani koda N500” “Wai kiyi me dashi?” “Abu zan saya” “Abu like?” “Anas ermm. Ermm” kasa fad’a masa tayi. Wayarta tajawo daga kan side drawer tayi typing abu a text bar ta mik’a masa wayar seda ya gama ja mata aji ya amsa karantawa yayi kamar haka; “Anas I need N500 please, I want to buy p...a...d.” “Ke wace erin mace ce? Ko Amal ma ta rik’e date nata kece baki rik’e ba? Ina zakije ki saya yanzu?” “Ba ruwanka bane, ni kawai kabani kud’in.” Tsuka yaja ya mik’e tare da zira jallabiyansa ya fice. Kuma ina zeje ta tambayi kanta. _25 minutes later..._ Dawowar Anas kenan, shinfid’e a k’asa ya tarar da Fannah se juyi take. Da wuri ya nufe ta tare da d’ago ta “cikin ne?” Kai ta gyad’a masa. “Sannu kinji? Ko zamuje asibiti?” “A’a zuwa anjima ze dena, please kabani kud’in inje in siya kaji?” “Gashi” ya mik’a mata ledar hannunsa. Tana dubawa taga pad d’inne har guda biyu. Dad’i taji sosai “thank you.” Tayi tayi ta mik’e amman ta kasa daga k’arshe shi yayi assisting nata yakaita bathroom d’in sannan ya bata space bayan minti biyar tafito se wani rik’e cikin ta take. Coffee ya had’a mata dukda be k’ware ba, sosai tayi appreciating ta shanye duka tare da masa godiya. Ajikinsa ta kwanta har tayi bacci. Se k’arfe 9:30AM Fannah ta tashi sema yanzu ta tuna Anas nada office. “Ya Salam!” ta fad’a a fili. “Anas! Anas ka tashi.” A hankali ya bud’e idanunsa. “Ciwon be dena bane har yanzu!” “A’a da sauk’i, Anas barakaje office bane?” “Yes se gobe.” “Why?” “You are sick I need to take care of you.” “But An-” “Shhh! lets go back to sleep.” Hannunta yaja ta fad’a jikinsa ya matseta gam tare da cigaba da baccinsa. *© miemiebee* [12:56, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 6⃣1⃣ ★‡★‡★‡ PRISON HOUSE MAIDUGURI, BORNO STATE. K’aramin gate ne ya bud’u Ya Khaleel ya sa kai ciki, be tsaya ko ina ba se wajen da aka tanada dan masu visiting prisoners. Da zamansa befi minti biyu ba aka bud’o wa Farouq k’ofa sanye yake da orange T-shirt na ‘yan prison meh ‘32’ rubuce a ta bayan. Sosai ya rame yayi bak’i, ta gefen bakinsa yanka ne alaman fad’a dawani yayi har yasamu injurin. K’arisowa yayi a kasalance ya zauna a kujera opposite Ya Khaleel. “Subhanallahi Farouq meya sameka anan?” Ya Khaleel ya tambaya cike da damuwa yana tab’a gefen bakin Farouq. Hannu yasa ya kawar da hannun mahaifin nasa “ba komai.” “Kamar ya ba komai Farouq da wanne kakeson inji ne? Da rashin ka kokuwa da rashin jinka? Cikin nan d’in ma baraka bar fad’a ba?” “Baba niba fad’a nayi ba” ya fad’i cikin murya cike da takaici. “Allah shirya min kai Farouq” hannu yasa ya d’ago wata leda tare da azawa kan table d’in yana bud’ewa. Abinci ne mai rai da lafiya, ga kaji kota ina. Ba makawa Farouq yasoma chi dan ko rabuwansa da abinci me kyau about a week now tun komawar Babansa Bama. Seda yayi dam ya kora da cool malt drink sannan yajisa d’an dadai. “Baba ya batun kud’in bailing nawan? Nagaji da zama anan.” “Farouq kasan kud’in bailing nakan ba abu neba na wasa, gun aikinka nayi masu bayani ko zasu d’an ji k’anka, albashin ka suka yanke sunce ba ruwansu dakai. Banki kuma sunk’i bani loan saboda ba aiki nakeyi ba, bakuma wani abu nayi possessing ba.” “Baba amman wannan abu is not fair, menayi da wannan Fauzin zesa a rufe ni?” “Saboda kai talaka ne Farouq shikuma yanada kud’i. Kai baka gani bane? Ba lawyer’n dayakeson tsaya mana kan case d’innan da zaran sunji Mr. Fauzi ne opponent d’in se su soma mana wasa da hankali.” “Bawani Mr. Fauzi dan ubansa, Fauzi kawai in bare amsa bakuma chan masa, uwarsa da Mr d’in. Wallahi na fito he must rule the day he was born.” “Ai fitowanka ba nan kusa ba Farouq.” Cike da rashin fahimta Farouq yace, “what do you mean Baba? Ina dubu d’ari biyar da muke dashi a k’asa?” Kai kawai Ya Khaleel ke girgizawa. “Baba talk mana, ina yake?” “Farouq a hanya na, na komawa Bama b’arayi suka tsare mana mota suka k’wace duka d’ari biyun danayi aiki na samu da k’yar sesa kajini shiru through out last week.” “What?!” Ya fad’a a tsawace tare da zabura. “Farouq yi hak’uri ka zauna.” “No! No! Baba this is unacceptable wallahi nagaji da zama anan. Nagaji, I can’t take it anymore. Yaushe ne zaka samu miliyan d’ayan da suke buk’ata ka cireni anan? Mschww!” “Calm down Farouq-” katse Baban nasa yayi. “No! I can’t calm down.” Mik’ewan shima Ya Khaleel yayi yace, “in har dan wannan baraka iya calming kanka ba then inaga there is no point ma in sanar dakai main abinda ya kawoni, ai wannan jaririn tashin hankali ne aganga da wancan.” Cike da rashin fahimta yace. “wanne kenan Baba?” “A’a barin fad’a maka ba tunda wannan ma yayi freaking naka out there’s no need in sanar dakai wanchan.” Hannun Baban nasa ya rik’e suka zauna atare. “Mene Baba please tell me. Ba abinda ze tada min hankali se lafiyar Fannah. Baba ina ba wani abun bane ya sameta?” Shiru Ya Khaleel yayi hakan ya bawa Farouq daman sake magana, “Baba talk mana please.” “Farouq inason ka kwantar da hankalinka ka sauraren da kyau.” Kai kawai ya gyad’a duk yakasa samun sukuni. “Jiya na je gidansu Fannah nake tambayan ‘yan gidansu ina take sabida ban ganta ba duk sukamin shiru ba wanda ya amsani I had to ask their neighbours nan ne suke sanar dani cewa Fannah tayi... Tayi...” “Tayi meh Baba?? Tell me!” yayi demanding “Farouq, Fannah tayi aure.” “Tayi meh?” Ya tambaya disbelievingly. “Tayi aure Farouq.” “No... No” kai yake girgizawa ba makawa. “Baba halan baka gane bane, Fannah is mine, she belongs to me no one can take her away. Whats mine is MINE, FANNAH TAWA CE Baba.” T shirt nasa ya yaga daga gefe d’aya tattoo ne d’an babba ya bayyana a saman hannunsa anyi zanen heart ciki kuma an rubuta ‘F&F’ ma’ana ‘Farouq and Fannah.’ Cike da mamaki Ya Khaleel ke kallon hannun d’ansa totally speechless. “Subhanallahi Farouq dan girman Allah me wannan? Tattoo ka zana a hannunka? Kana muslimi?” “Eh Baba” ya amsa sa confidently “and I mean it I will never rest se ranan da Fannah tazamo TAWA sabida TAWA CE dama. Koma waye ya aureta seya sake ta inkuma hakan be yuwu ba, I don’t care koda zanyi spilting blood. Fannah tawa ce, ba mahaluk’in daya isa ya k’wace ta.” Kai Ya Khaleel ya kad’a “koda kuwa mutumin Mr. Fauzi ne? Koda Mr. Fauzi ne mijin nata?” “Mr. Fauzi? Kana nufin shine ya auri Fannah matata???” “Shi ya aureta Farouq, Mr. Fauzi shine mijin Fannah, hak’uri ya zama 2 Farouq you can’t fight with Mr. Fauzi he is too powerful.” “Baba abu d’aya nakeson kamin, kawai kasan ya za’ayi in fita daga god forsaken place d’innan. Wallahi kaji na rantse sena koya wa Mr. Fauzi whats mine is mine and mine alone!” ya buga kan table d’in. ★★★★★ MAIDUGURI INTERNATIONAL HOTEL LTD. Kwance Fannah take bisa gado se kuka take duk tabi ta tadawa Anas hankali yarasa meke masa dad’i. “Fannah to muje asibiti mana” yace da ita cike da tausayi yana a zaune kan bediside drawer’n kanta. Kai kawai ta girgiza masa “zuwa gobe ze dena we don’t have to.” “Har se gobe? Tun safe ba abinda kikeyi banda kuka ko breakfast kink’i chi haka lunch ma. Ni ban zama care giver ba na gaji da kula dake, kimutu kika ga dama.” “Ai banche ka kula dani ba nima, tun farko ma banche ka zauna nan ba, kaje office abinka.” Ta juya masa baya. “Ai da kin fad’a hakan tun d’azu seda aka tashi a office d’in zaki wani cemin da ban zauna dake ba? Mschw!” Banza tayi dashi ta cigaba da kukan ta tana juye-juye. Ignoring nata yayi ya koma kan couch ya zauna tare da ciro wayarsa yana latsawa. Chan da kwanciyan kan gadon ya gagareta ta sauk’o k’asa se juyi take tana kuka, sekuma ta basa tausayi shi aduk lokacin da baida lafiya zata bar duk wani abinda takeyi takula dashi, why can’t he do thesame? Ajiye wayar nasan yayi ya taso zuwa inda take a kwance ya tsuguna. “Fannah” ya kira sunanta. Baya ta juya masa. “Fannah okay I’m I’m...” sekuma yayi shiru bayajin ze iya ce mata sorry. “Tashi kinji?” Nanma banza dashi tayi. “In had’a miki coffee?” “Don’t bother, banaso.” “Fannah bakici komai bafa since in the morning.” Shiru tayi bata ce komai ba. “Okay Fannah I’m sor-” be k’arasa fad’a ba yayi shiru. “Kinji?” “Banji ba.” “I just apologised to you, you have to accept it.” “Ni haka nake baka hak’uri ne? ka rik’e hak’urinka banaso.” “Okay I’m sorry kinji? Tashi ki koma kan gado.” Ba gardama ta mik’e ta koma gadon. Nan ya had’a mata yakai mata seda ya tabbata ta shanye yabarta ta koma ta kwanta. **** Washegari Fannah ta tashi garau masha Allah taji sauk’i sosai. A farko ma cewa Anas yayi bare je office ba, Fannah ce tasa sa a gaba saboda tasan halinsa duk wani alkhairin daya ma mutum seya k’arisa da tsiya, dan haka kawai tasa sa a gaba seyaje, shikuma dan nuna mata be damu da ita ba ya shirya yayi tafiyarsa ko breakfast yak’iyi. Yana ji tana kirar sunansa ya dawo su karya yayi banza da ita. Isarsa office ya baje kan kujera nan Kacallah yashigo masa da files ba adadi yasoma bi one-by-one yana signing, by 10:00AM yafita meeting sede tunda aka soma yakasa gane me akeyi kwata kwata hankalinsa bayya jikinsa yana chan yana tunanin Fannah for sure yasan ta samu sauk’i but he can’t stop himself from being worried, ana fitowa daga meeting d’in ya kirata a waya a lokacin tana bayi tana wanka seda tafito taga missed call nasa k’waya d’ya. “Shegen girman kai, ko kiran mutum sau biyu ma be iya ba” nan ta kirasa back bada dad’ewa ba ya d’aga. Shiru tayi bata ce komai ba shima haka sun kusan minti biyu shiru sannan yakira sunanta “Fannah.” “Na’am” ta amsa. “Aww dama kina kai? Shine bakiyi magana ba tun d’azu?” “Toh ai kai ka fara kira na.” “Ya jikin naki?” “Da sauk’i.” “Okay...” “Shikenan can I go ba k to what am doing?” “Me kikeyi?” Ya tambaya haka kawai yaji yanason cigaba da sauraron muryarta. “Yanzu nafito daga wanka zan shafa mai.” “K’azama se kusan to twelve na rana zakiyi wanka.” “Toh ai bacci nayi.” “K’azama ba.” “Niba k’azama ce ba, excuse me zan shafa mai nan ta katse.” Murmushi dukansu suka tsaya yi suna kallon wayoyinsu musamman ma Fannah. She can’t deny it anymore ta fad’a tarkon soyayyar Mr. Fauzi sede batason soyayyar yaje ko ina saboda batasan ayi hurting nata daga k’arshe ‘cause muddin Anas yasan sirrinta he will run away and leave her, aduk lokacin data tuna da wannan seta yayyafa wa zuciyarta ruwan sanyi dan huchar da zazzafan son Mr. Fauzi. Haka har tagama shirinta tana tuna jiya yadda Anas ya riga mata hidima ko da daddare da take kuka ya hana kansa bacci ya zauna da ita yana pompering nata, haka kawai taji tana murmusawa. Shima Anas zaune yake cikin one of hotels daya saba chin abinci, ga abincin agabansa amman yakasa ci se murmusawa yake musamman ya tuna rananda take tsaye da towel a gabansa dakuma lokacinda cinyoyinta sukayi tsami yake shafa mata muscle pain reliever. Da k’yar ya iya ya kai spoons biyar yaji yama k’oshi tunanin Fannah kad’ai ya ciyar dashi. Be jira aka tashi ba yabar office ji yayai kawai Fannah yakeson sawa a idanunsa, it hasn’t been long amman seji yake like shekara da shekaru ne. _K’arfe 3:00PM_ Tsaye Anas yake bakin hotel room nasu ya kasa shiga dan girman kai. “What if tace mena dawo yai since before lokacin tashi yayi, me zance mata? That I miss her I want to see her? No! No way ai seta raina ni ta d’au ko sonta nake.” Ya juya ze koma kuma yaji bare iya ba Fannah yakeson gani and no one else. Seya d’aga hannu zeyi knocking seya sake maida hannun nasa baya. Fannah kuwa tayi waya da Afrah ta buga game, ta kalli pictures na bikinsu, tayi kallo, tagaji zaman shirun ya isheta. Sanin ba kowa a floor dasuke daga ita se Anas, Anas kuma baya nan ba wanda ze hauro ta d’au wayarta kad’ai. Atamfa ne d’inkin fitted riga da skirt ya mugun mata kyau a jikinta, kayan ya zauna tip tip. D’aurin ta ta daidaita sannan ta bud’e k’ofar, baki ta sake ganin Anas tsaye jikin k’ofar. Mutuwan tsaye sukayi duk a wajen suna kallon juna sun kusan minti biyu suna abu d’aya sannan ta kawar da kanta zata rufe k’ofar dan komawa ta d’auko mayafinta kenan Anas ya rik’o hannunta. Be d’aga idanunsa daga kan k’irjinta ba har ayanzu se kallonta yake. “Uhm Anas kasakeni in d’au mayafi na please.” “Why?” Ya tambayeta se anan ya dawo da kallonsa kan kyakkyawar fuskarta data sha d’an light makeup. “Anas hakan ba kyau-” katseta yayi. “No I like it this way, kinfi kyau haka kar ki rufe jikin ki kinji?” “But Anas-” katse ta ya kuma “Fannah I’m your husband nace nafison ganinki haka” se yanzu ya tuna da kalamun ta na ranan cewa batason tsinuwan mala’ikun rahma. “Ko ki zauna haka kokuma inyi fushi dake mala’ikun rahma suyita tsine miki.” “A’a dan Allah don’t talk like that kaji karkayi fushi.” “Zaki zauna hakan?” Kai ta gyad’a a hankali. “Good” ya saki brightest smile nasa. “Da ina zakije ahakan?” “Babu kawai nagaji da zaman cikin ne nace barin d’an lek’o waje.” Ta basa amsa tana k’oka’rin raba hannunta da nasa. “Shine zaki fito ahaka ba hijabi ba mayafi?” Ya fad’a a little bit pissed off, daga yadda yake magana za’a san kishi ya motsa. “Toh Anas naga ba kowa a floor d’inmun, mu kad’ai ne.” “I know what of room services? Insuka hauro alokacin da kike k’ok’arin fitowa ahaka fah? Se suganki?” “Yanzu fa kace nafi kyau a haka kar insa mayafi.” Hannu yasa ya hargitsa gashinsa cike da haushi. “For goodness sake Fannah I’m your husband, taya zaki had’ani da room service? Nine kad’ai am aloud to stare at your body and not them.” “I’m sorry” tace dashi tana kallon k’asa. “No you are not Fannah, daga yau karki sake fitowa koda bud’e k’ofa ne ba hijabi ko mayafi do you get me? Banason mayafin ma hijabi constant kinji?” “Haba mana Anas ai dan bud’e k’ofa kam mayafi ma yayi.” “Ni bemin ba banaso, Fannah I’m serious.” “Okay naji barin k’ara ba.” “Better” yace yana hararta. “Matsa min in wuce.” “Ka wuce ina? Anas lokacin tashi daga office fa beyi ba, meka dawo yi?” “Me ruwanki? Ko kin d’au wai dawowa nayi saboda nayi missing naki? Hell No nadawo d’aukan wasu files ne, mema zan kalla a fuskarki ko jikin naki, excuse me?” “Niba abinda nake nufi ba kenan” gefe ta matsa masa ya shiga tabi bayansa. Briefcase dayake adana files nasa ya ciro shi a dole yadawo ne dan d’auko abu tana tsaye akansa se dube-dube yake yakasa koda d’aukan d’aya ciki. Ganin har yaci minti biyar be samu ba Fannah tace, “Anas anya kuwa files d’in kazo d’auka ba wani abu daban ba?” Da biyu tamasa tambayan dan kuwa hankalinta ya bata ba file yazo d’auka ba wayasani ma ko missing nata yake dagaske tunda har ya bud’e baki yafad’a d’azu indirectly. “Mind your business mana meh ruwanki da abinda nakeyi kin wani zo kin tsaya min akai sekace soldier (soja.)” “Allah baka hak’uri niba abinda nake nufi ba kenan, I was thinking ko kanaso in tayaka nema ne.” “Neman meh?” “File da kake neman, koba file kace kana nema ba?” Shi se yanzu ma ya tuna eh file yazo nema. “Toh banaso, zan nemi abu na dakaina.” “Yi hak’uri in taya ka” tace dawani mocking smile tattare da fuskarta. “Fannah yaushe na soma wasa dake? Mind your business.” Juya baya tayi tasoma tafiya zata kan couch ta zauna. “Mutum bare fito fili ya fad’a meya kawo sa ba se shegen zurfin ciki” tace chan k’asa k’asa almost kamar da kanta take maganar. Bejita gabad’ai ba amman yaji some part. “Ke! Me kikace?” Take ta juyo dan bata tsamman yajita ba. “Babu kawai cewa nayi Allah sa kasamu file d’in.” Harara ya galla mata tare da cigaba da nan file dayayi qarya yana nema. Chan ya d’ago kai yaga se lastse wayarta take, tsayuwa yayi yana kallonta ko kyafta ido baiyi data d’ago kai seya juya daga k’arshe ya ciro wani file yayi hanyan fita ai dagangan ya sakar da k’ara “awwchh! My ankle.” ya tsuguna yana rik’e k’afar. Da sauri ta nufa wajen “Anas meya faru?” Ta tambaya tana dubansa. “My ankle nakega nayi spraining. Awcchh!” “Ya Salam! But how?” Ta tambaya. “Nima bansani ba, argh!!” Hannunta ta zagaye ta bayansa tayi assisting nasa ta kwantar dashi kan gado. Se faman “awch!” na k’arya yake, sam yaji bayason rabuwa da ita koda na second ne shiyasa yayi coming up da wannan plan na spraining ankle nasa. Takalmasa ta cire masa da socks d’in, da ta tab’a k’afan hagun nasa seya sa ihu. ”Sorry, d’an tsaya in gani.” “A’a barshi.” “Anas kasan fa bareyi abar k’afar haka ba, nida cinya na sukayi tsami kwanaki ba haka kasani a gaba ka riga shafa min man zafi ba? Ka tsaya inga.” K’afan nasa ta aza kan cinyarta tana d’an mammatsa wajen ankle nasan. Sekuma abin yasoma masa cakulkuli, dariya yakeson yi amman ya matse se faking “awch!” Yake tayi. “Amma Anas banga alaman koda b’ullowan muscle bafa, kuma kace kayi spraining.” “Aww maqaryaci kikeson cemin komeh?” “A’a kawai de da abun ban mamaki ne.” “Sakemin k’afa ba sekin zagen ba.” Nan ya d’aga k’afarsa daga kan cinyar tatan. “Anas ba abinda nake nufi ba kenan I’m sorry.” “Banaso, tashi kibani waje.” K’afar nasan ta mayar kan cinyarta. “I’m sorry kaji?” “Naji” yace ba tare da ya kalleta ba. “In shafa maka magani awajen?” “No you don’t have to.” “Anas in ba’a shafa ba baraka iya taka k’afan bafah.” “Don’t worry just come lets sleep.” “Sede inkai ni banjima da tashi daga bacci ba.” Nan ta mik’e ta rage masa kayan jikinsa ta juya kenan ya rik’o hannunta “lets sleep kinji?” Be jira amsarta ba ya jata ta fad’a jikinsa. “Anas me haka?” Ta fad’a a lokacinda take k’ok’arin tashi. “Lets sleep.” ya sake matseta jikinsa. “Ahaka? Ai namaka nauyi barin kwanta a gefe kaji?” “No I want it this way.” Bata sake cewa komai ba sede sam ta kasa samun sukuni, wani erin baqon yanayi ta tsinci kanta ciki. _20 minutes later..._ “Anas” ta gwada kiran sunansa jin yayi shiru, ta d’aga hannunsa daya zagaya akan bayanta a hankali sannan ta taso daga jikinsa ta yadda bata tadashi daga baccin nasa ba. *© miemiebee* [12:56, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 6⃣2⃣ *YEYYY! ALHAMDULILLAH SISTERS FOR YOUR WARM PRAYERS, JIKIN MAMA DA SAUKI, ANYI OPERATION AND IT WAS A SUCCESS* Suit da shirt nasa data cire d’azu ta d’au tasa a laundry basket. Bayan ta dawo tana tsaye akansa ta gwada tab’a k’afar sa dayace yayi spraining to her suprise taga beko motsa ba, sake tab’awa tayi da d’an k’arfi nanma be motsa ba se baccinsa yake. Mamaki ne ya rufeta mutumin dayace yayi spraining k’afar ne ana tab’awa amman baiko jin zafi? Lallai kam! Komawa kan side drawer’n gefensa tayi ta zauna tana k’ure masa kallo daga gashin girarsa, idanunsa hanci dakuma lips nasa, batasan seda takai hannunta kan lips nasa ba haka kawai taji tanason ta tab’a, taji tanason tab’a lips nasa masu uban fidda bak’ak’en kalamu ganin yad’an motsa ta miyar da hannun nata baya haka tata kallonsa har seda La’asar prayer yashiga. “Anas!” takira sunansa a hankali. “Anas katashi lokacin Sallah yayi.” Nanma shiru seda tasa hannu ta tab’a sa ya bud’e ido ya azasu kanta. “Lokacin Sallah yayi” tace tare da kawar da kanta. “Kefa barakiyi ba?” Ya tambayeta dan kwata kwata ya manta batayi. Yi tayi kamar bata jisa ba ta mik’e. “Yes?” Cewar Anas. “Anas banayi ka manta ne.” Ba tare da yace da ita komai ba ya mik’e kan gadon kwata kwata ya manta da k’aryan spraining ankle nasa daya mata, garau ya mik’e yana tafiya. Baki ta sake tana kallon ikon Allah. “Anas har k’afan ya warke ne?” Se a yanzu ya tuna ya mata k’arya kuma tariga ta gano gaskiyar. “Da sauk’i be warke ba” yace da ita yana basarwa tare da d’an karkata tafiyar tasa. Daga yadda take kallonsa yasan tagano gaskiyar no point ya cigaba da k’aryan. “Okay, okay naji you caught me lying actually ba spraining ankle d’ina danayi I just faked it are you okay?” Dariya sosai ta b’arke da, Anas be tab’a ganinta tana irin wannan dariya ba se yau and he find her cute, admiring nata ya tsaya yi se dariya take harda ‘yar hawaye se chan tad’anyi shiru. “I’m sorry” tace tana girgiza kai hannunta na akan cikinta. “Kin gama?” Yace da ita. “I’m sorry but Anas why do you have to lie?” “Nima bansani ba, meh ruwanki?” “Anas daga tambaya.” “I miss you thats it” yace da ita sincerely dan dama haka yake he is straight forward. Wani irin yanayi ta tsinci kanta ciki a yayinda bugun zuciyarta ya k’aru. She couldn’t help it batasan seda ta soma blushing ba. ‘yar k’aramar tsuka yaja; “Mschw! you can stop blushing, not anymore I don’t miss you again” daga nan ya shige bayi tana zaune kan gado har ya idar da Sallah. Abinci yamusu ordering bayan da suka gama ci ta d’au towel nata da hijabi ta nufa bayi dan sake watsa ruwa tad’an kwanta kafin Maghrib. A yayinda ya cigaba da gudanar da harkar gabansa a laptop shikuwa, bayan like 2 minutes ya tashi ya fice bada dad’ewa ba ya dawo yatsansa na yoyon jini da alama yankewa yayi. A gurguje yashigo d’akin, bayi ya nufa ya bud’e kasancewar Fannah batasa lock ba. Idanunsa basu sauk’a a ko ina ba sekan Fannah dake wanka, kwata kwata ta rasa me ya hanata sa lock bakin k’ofar a tunaninta wai ai Anas yasan tana ciki bare bud’e taba shiko yankan da yayi yasa ya mance da tana cikin bayin. Seda ya k’are mata kallo sama da k’asa sannan tasa wani irin masifaffen ihun da bata tab’ayin irinsa ba. Hannu yasa yakai baki kan wanda zeyi amai sannan da wurwuri ya rufe k’ofar. Both of them were speechless for the mean time, Fannah can’t believe Anas yaganta a haka kamar yadda shima yakasa believing yaga Fannah ba komai a jiki. Kuka tasa a bayin wanda har shi Anas d’in ya jiyota, tissue yaja ya tare zubar jinin sannan ya dawo kusa da k’ofan ya tsaya yana sauraron sautin kukanta, yarasa nayi ganin bata da niyyan barin kukan yakira sunanta “Fannah.” K’arfin kukan nata ta k’ara. “OMG! Fannah kukan me kuma? Stop crying please.” Banza tayi dashi takoma cikin jacuzzi ta zauna se kuka take. “Fannah stop crying na manta kina ciki ne, kinji?” Nanma bata ce komai ba. “Kema mesa baki rufe k’ofar ba?” Cikin sautin kukan tace, “toh ai naga kasan da shiga na, kawai kawani kama ka bud’e mutum...” ta fashe da kuka. “Fannah ai ba da gangan na bud’e miki ba na manta ne.” “Bawani mantuwa wallahi...” ta k’are maganar cikin kuka. “Toh acewarki zan bud’e ki ne da gangan? Mezan kalla a jikin naki? Mschw!” ya fad’a a tsawace. K’arfin kukanta ta dad’a. “Okay, okay I’m sorry I should have knock still, bar kukan kinji?” Batace dashi komai ba tacigaba da rera kukarta. “I said I’m sorry, kinji?” Nanma shiru. “Ko sena shigo zakiyi shirun?” Still batace komai ba. Handle na bayin ya waina. “A’a dan Allah karka shigo” ta fad’a cike da tashin hankali, k’ok’arin jawo towel nata take amman takasa. Murmushi kad’an ya saki, ,“zakiyi shirun?” “Eh zanyi, nama nayi, nayi dan Allah karka shigo.” Daga nan ya koma kan gado ya zauna yana jiran fitowarta se canza tissue yake jinin bebar zuba ba har yanzu. Tuntuni Fannah ta gama wankan amman tak’i fitowa batasan dawani idon zata sake kallon Anas ba. Har yanzu takasa believing abinda ya faru d’azu. Ganin about 10 minutes har yanzu tak’i fitowa Anas yace, “Fannah wai haihuwa kike cikin barhroom d’inne?” Chan k’asa k’asa tace, “bansani ba wallahi da kallon tsireci ba haramun bane dana rama nima, nasan dagangan ka bud’eni.” “Fannah I will open the door in baki fito ba.” Ya fad’a a lokacin dayake takowa zuwa bakin k’ofar. “I have a cut on my finger I need to wash it ki bud’e.” Tana jinsa tak’i koda motsawa, tsaye take sanye da hijabinta gaban mirror. “I’m couting to three in baki bud’e ba I will saboda nasan kin gama wankan tun d’azu. One... Two...” Duk tana tsaye tana jinsa “Three!” Karap ya bud’e k’ofar tsaye yaganta gaban mirror “awww kinaji na dama?” A ranta tace kad’au yanzun ma ba kaya zaka ganni ko? Seka koma. “Fannah I’m talking to you.” Ko d’ago kai ta kallesa batai ba dan batason sake had’a ido dashi gefensa tabi ta fice nan yayi treating ciwon nasa yafito shima. Bayan fitowarsa ya tarar da ita zaune kan gado tayi jugum ga d’an hawayen dake forming cikin idanunta. A farko yayi niyyan ignoring nata sekuma ta basa tausayi, itan da ko cinyar ta batason agani bale ache duka aka ganta. Takowa yayi zuwa gabata batako noticing nasa ba saboda yadda tayi zurfi cikin tunani. “Fannah” ya kira sunanta a nitse, nanne hankalinta ya dawo jikinta kai ta d’ago, idanunsu na had’uwa tayi saurin kawar da kanta tare da sa hannu tana share hawayenta. Mik’ewa tayi dan ciro mai nata ta shafa tazo bin gefensa kenan ya rik’o hannunta tare da dawo da ita baya. Kukan da take k’ok’arin had’iyewa ta soma, kallonta ya tsaya yi be hanata yiba seda tayi me isarta sannan yasa hannu yana share mata hawayen. “I said I’m sorry I didn’t mean for it.” yace cikin wani irin salo. Kai kawai ta gyad’a masa tana k’ok’arin karb’an hannunta. “Baki hak’ura ba?” “Na hak’ura” tace ba tare da ta d’ago kai sun had’a ido ba. Hannu yasa k’ark’ashin hab’anta tare da d’ago ‘yar fuskarta yana kallo har a yanzu tak’i barin su had’a ido. “Fannah you’re not, look at me” k’in kallonsa tayi. “Please...” anan ne ta d’ago idanunta ta azasu kan fuskarsa “I’ve looked at you, shikenan?” Tasa hannu ta sauk’e hannunsa daga fuskarta. Gefensa tabi ta d’au mai nata zata shiga toilet dan shafawa ya dakatar da ita ta hanyan kiran sunanta. Chak ta tsaya “I’ll excuse you kinji? You don’t have to go in there.” Be jira jin me zatace ba ya fice, ajiyar zuciya ta sauk’e. A nitse tasamu ta shafa manta tasa wani sabon atamfa d’inkin riga da skirt tagama shirinta tsaf sannan ta mik’e a kan gado. Har ayanzu Anas be dawo ba, da kwanciyarta bekai da minti biyu ba akayi knocking bisa k’ofar. Tashi tayi dan bud’ewa seta tuna da dokar da Anas ya kafa mata seda tasanya hijabi sannan taje ta bud’e. Tsaye ta tarar da Anas, “can I come in?” Ya tambayeta. Kai ta gyad’a masa tare da matsa masa. Bayan ya shiga ta rufo k’ofar tare da ajiye hijabin a gefe, tayi miqarta kan gado. “kishirya Amal said she wants to see you.” Dama zaman nan d’in ya isheta ba musu ta mik’e ta soma shiri shima haka. Mayafi kalan atamfarta ta yafa duk Anas na kallonta seda ta gama shirin sannan yace, “ina zakije ahaka?” “Kamar ya ina kuma? Kaifa kace Amal wants to see me.” “I know I mean da wannan shirin.” Ya nuna ta da hannu. Kallon kanta tayi up to down bataga wani abin aibantawa ba. “Anas wani abu ne?” “Yes kisa hijabi baraki fita da wannan gyalen ba.” “Anas gidanku fa kace zamuje ba wani wajen ba” “Nasani nide ki cire kisa hijabi.” “Haba mana Anas nan da gidan kun ma sena sa hijabi ai naga bawani gun zamuje ba gidanku fa zamuje, waze kalleni achan?” “Shettima da me gadi zasu kalleki nikuma banaso.” “Yanzu Anas kishin Shettima kakeyi?” Ignoring nata yayi ya nufa wajen akwatunanta, medium red d’in ya bud’e sannan ya d’ago kai yaga kalar atamfar tata yaciro color’n hijab daze shiga dashi. Daga nan ya nufa wajenta mutuwan tsaye tayi takasa koda motsawa se binsa da kallo kawai take. Gyalen nata ya cire ya ajiye a gefe “gashi sa wannan lets go.” Se ayanzu hankalinta ya dawo jikinta “but An-” “Fannah banason surutu just wear it” ta gefen idanunta ta watsa masa harara sannan ta cire d’an kwalin nata ta b’urma hijabin. “Perfect!” yace a lokacin dayake kallon ta. “Lets go” ba abinda Fannah ke banda bin Anas da harara ahaka har suka isa zuwa wajen motarsu ya bud’e mata tashiga sannan ya rufe. ★‡★‡★‡ Haka de rayuwa tacigaba da kasance ma Anas da Fannah. Anas yana tsantsan kishin Fannah, ko kad’an bayason wani d’a na miji yagane mata jiki musamman inya tuna ranan da ya ganta a bathroom. Shi karan kansa yasan yasoma sonta yanzu saide bayya tsammanin ze tab’a fad’a mata ‘cause har a yanzun bawai yayi accepting bane yasan sarai da ze samu wani yayi mai bayanin how he feels towards Fannah cemasa za’ayi yana sonta, abinda bayya son ji kenan. Sesa har ayau yak’i yarda wai sonta yake. Ko zaune yake a office muddin da pen a hannunsa bai sanin seda yake soma rubuta sunanta akan paper, a kullum burrinsa yadawo hotel nasu ya samu Fannah. Ta b’angaren Fannah ma duk kanwan ja che, sede ita tayi accepting son da take masa amman kuma barata bari son yaje ko ina ba saboda rashin martabar ta, she don’t want to be broken. Ba laifi Fannah da Anas suna shiri yanzu danko se su d’au kwana biyu basuyi fad’a ba amman gasa bak’ak’en kalamu kam na nan, da abun ya tab’o Mr. Fauzi kuwa se yayi dalilin dazesa zasuyi fad’a at the end kuma yazo yana bata hak’uri. ***** Da bikin auren Anas da Fannah wata d’aya cus kenan, cikin wattani shida dasukayi agreeing akai. Anas ya biya Fannah first salary nata wanda yake N500,000 duka ta d’au ta dank’ala wa Mami akan sukai Baba National Hospital Abuja a dubasa dakyau amasa duk wani abinda ya kamata. Koda da Mami ta tambayeta a ina tasamu uban kud’i haka ce mata tayi Anas ne ya bata shiko koda da Mami takira sa dan masa godiya be nuna mata wani abu ba. Alhamdulillah! Su Mami sunje sun dawo lafiya qalau da zaran Baba ya shanye magunansa ana fatan masa waraka. **** Yanzu Fannah take gama had’a musu kayakinsu ansamu an gama masu sabon gidansu, she is super excited taga gidan musamman ma dataji Anas ne ya zana da hannunsa. Bayan ta gama had’a musu kayakinsu duka yasa aka sauk’o masu dashi aka kai mota wajen biyan bills ya nufa yayi settling. Fannah na zaune a mota tana jiransa. “Lets go?” Yace da ita alokacin daya kunna motar. Kai ta gyad’a masa cike da jin dad’i “yes.” Unguwar Giwa Barack yajasu chan inda sabon gidansu yake, daidai gabar wani mansion Anas yasa kai, gate d‘in na identifying plate number’n motar nasa seya bud’u da kansa. Baki Fannah ta sake cike da mamaki, kasa b’oye mamakin nata m tayi ta tambayesa. “Anas dakansa yake bud’uwa?” Be amsata ba seda yayi parking a lot sannan yace, “yes ‘yar k’auye dakanshi yake bud’uwa dakuma kulluwa muddin anyi registering plate number’n.” “Owwww!” tayi exclaiming tana gyad’a kai. “In d’an wannan kina sake baki nakega by the time muka shiga ciki zakimin littering marble floor na miyau.” Harara ta galla masa ta gefen ido. “Lets go in” yace da ita. Atare suka fito ta tsaya k’are wa gidan kalloi, flat mansion ne me penti fari daga sama se divider milk k’asan kuma brown, tunda Fannah take bata tab’a ganin gida katafare me kyau ba kamar wannan ba sede a TV show. Juyowa yayi ya kalleta seyayi murmushi ganin yadda ta kasa rufe baki, hannunta ya fisga “lets go” wajen garden yasoma kaita gabad’ai wajen green carpet ne seda coloured flowers wanda suka sake k’ayata wajen, a gefe guda kuwa bishiyoyi ne da dama kamarsu guava, mango, banana, dates (dabino) da sauransu. Gaba da wajen kad’an aka yi wani ‘yar runfa me kyan gaske, cikinsa tables ne guda biyu da kujeru hud’u-hud’u a kowanne. Daga gun garden ya wuce da ita swimming pool an k’ayata sa sosai, daga chan suka sake dawowa gaban gidan inda yake ajiye motocinsa da ko plate number ba’a sa musu ba alaman na kwalya ne bawai na hawa ba. Sabin motoci ne pil sauran ma ko b’are ledojin jikin ba’ayi ba, irgawa ta soma da Anas ya gano haka seyace “ba sekin b’ata lokacin ki ba guda 7 ne kacal lets go in.” Haka yajata zuwa main door d’in. K’ofar kad’ai ma abar kallo ce. Irin manyan security doors d’innan ne. Password d’in yasa anan k’ofar tayi kukan “welcome home Mr. Fauzi and unknown.” Nanma seda Anas ya rufa ma Fannah baki yau tana ganin ikon Allah k’ofa na magana. ‘Yan danne danne yayi jikin k’ofar se ya sake managa “Mrs. Fauzi added to family list, welcome home.” A hankali ya bud’u suka shiga ya sake rufe kansa. Kaftareren parlour ne da had’ad’d’un frames, wallpaper da verses, cushions na cikin farare swal seda colourful throw pillows jere akai. Rug d’in dake parlour’n na nan colourful shima. Cinema (babban TV) ne manne jikin bangon kai tsayuwa dan bayanin had’ewan gidan youngest billonaire b’ata lokaci ne ayita imagining kawai nagaji(LOL) Haka yabi ko ina cikin gidan ya nunnuna mata Fannah de takasa magana har a yanzu inbanda wow datakeyi ba abinda ta iya tace, jacuzzi ko ina cikin bathrooms banda d’akin Anas dake nan harda Live CNN connected ciki. Bayan da suka gama biye ko ina cikin gidan suka sake dawowa parlour, daba dan Anas ba da Fannah ta b’ace cikin gidan danko ta manta hanyan da suka bi. “So kinga d’akin ki ba? The purple one, nikuma nawa ne farin, we will no more be sharing a room.” Cewar Anas, da biyu yayi maganan danko yasan sarai Fannah da uwar tsoro barata iya kwana ita kad’ai a d’aki ba. Idanun ta ta d’aga ta aza akansa. “Eh nagani this is a wonderful house, kudos to you. Amman Anas nikad’ai zanna kwana cikin makeken d’akin chan??” Ta tambaya tana zaro idanunta. “Yes ke kad’anki-” katsesa tayi. A’a dan Allah Anas wallahi barin iya kwana ni kad’ai ba kayi hak’uri please, ko a k’asa ne a d’akin ka zan na kwana.” “Why?” Ya tambayeta yana me jin dad’i amman se nuna ma ta yake kamar bayyaso. “Anas a list na contract namu ai bakace za’a na raba kwanciya ba, kuma kafa san mutumin, wallahi ze dawo dan Allah karka min haka.” Cruel smile ya saki, “I will think about it.” “Anas please...” Ta rok’esa. “Okay naji” yace ganin zata soma masa kuka. Dad’i taji sosai wanda ta kasa b’oyewa. “Ermmm... Anas nace d’akuna nawane a gidan duka?” “Ke wani irin brain ne dake daman ba k’irgawa naga kinayi ba d’azu?” “Nafara irgawa sena rikice.” Kallonta yayi ta gefen ido, “fish head” yace a hankali. Sarai tajisa amman tayi shiru. “Guda 7 ne including guest room seda parlour biyu dakuma toilets 7 se kitchen d’aya da store room biyu. Clear?” Kai ta gyad’a a hankali tare da had’iye miyau. Sede daya kalli fuskarta ya gane tanada tambaya. “Say it out”,yace da ita. “Ermm. Anas duka d’akuna 7 d’in zanna sharewa ni kad’ai?” “Eh da meh aikin ki? Aure fa kikazo yi ba hutu ba Fannah.” “Anas nasani amman...” se kuma tayi shiru “kad’an taimaka please ga shara ga mopping gakuma girki yi hak’uri.” Murmushi ya saki wanda fararen hak’waransa na sama kad’ai suka bayyana. “Karki damu akwai masu aiki zasu na zuwa morning and evening suna duk wani aike-aiken, abinda zakina yi kawai cooking ne dan ba daga hannun kowa nakecin abinci ba, kema se kinyi sanitizing hannunki tukuna, clear?” *© miemiebee* [12:57, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 6⃣3⃣ *Assalam, as I promised zan bud’e new blog address, I did and its* beeenovels.blogspot.co.ke *so to my blog readers lets hit! Thanks for the love and support and also for the warm prayers, love you all!* *Also masu cewa nayi repeating page 62 twice a’a ku gane mutane ke yi ba ni ba, ina miyar da hankalina sosai wajen numbering pages so take note bana mistake anan. Masu editing min pages nasan kwad’ayin son next page ke saku yi amman kuyi hak’uri ku dena please kuna janyo confussion* Kallonsa ta tsaya yi danko be isheta da kallo ba wai har setayi sanitizing hannu tukuna ta masa girki, shima kallon nata yake da gira d’aya a d’age. “Baki jini bane? Nace you need to sanitize those hands” ya kalli hannun nata “before cooking for me” Kallonta ta kawar daga garesa ba tare da tace komai ba. Taku d’aya ya k’ara kusa da ita tare da rufe gab dake tsakaninsu da sauri tayi taking step backward, ganin haka ya k’ara 1 step forward haka suka tayi seda yakaita jikin bango, wani irin kallon tsiya yake mata da tuni yasa zuciyarta bugawa fat-fat. “Kinji ni?” Yasake cewa da ita alokacin dayake kallon lips nata. Kai ta gyad’a cike da tsoro “nn... Na... Naji.” bending wuyansa yayi ta hanyar matso da fuskarsa kusa-kusa da nata dududu ratan dake tsakaninsu befi inchi d’aya ba. K’ara dad’uwa bugun zuciyarta yayi a yayinda k’arfin numfashinta ya dad’u. “Anas pl-” bata k’are maganar ba ta matse idanunta gam ganin Anas yasake matso da fuskarsa kusa da nata, har had’ewa numfashinsu yake. Juyawa tayi zata bi gefen damanta dan guduwa, karap ya aza hannnsa jikin bangon ya dakatar da ita, haka ma yayi a gefen damanta “Anas please ka ba-” bata k’are maganar ba taji ya kunna switch d’in wuta daga jikin bango tare da matsawa baya. Shu’umin murmushi ne fal d’auke a fuskarsa “Da me kika d’au zan miki? LOL such a negative thinker. You thought I’ll kiss you right?” Wani irin kunya taji ya rufeta ji take kamar ta tone k’asa ta b’oye kanta, gabad’ai ta gama tsorata ta d’au kissing natan zeyi, amman dan iskanci ze kunna wuta shine seyayi kalan abinda ya mata? Mschww. “Ni ba abinda nake nufi ba kenan” ta fad’a dan kare kanta tana kallon k’asa. “Whatever ba sekin min k’arya ba.” ya fad’i da wani murmushin tsiya fal a fuskarsa. Ganin batada abinda zata ce masa kawai ta fara tafiya dan barin parlour’n although batasan ina take dosa ba. Kallonta yake ganin ta d’au hanyan store room ya tsayar da ita ta hanyan kiran sunanta, “Fannah!” Banza dashi tayi tana me cigaba da tafiyarta. “In d’akin ki kike nema that is not the way, you go right” ya nuna mata da yatsa. Bata ko tanka sa ba tabi right d’in ta fice. Achan ta samu d’akinta. Akan gado ta zauna se kai take girgizawa ta matse idanunta gam har a yanzu kunyan abinda ya faru tsakaninta da Anas d’azu take. Tsuka taja a fili “mscwh! Ai seya d’au dama tunba yau ba ina expecting kiss daga garesa, Ya Salam!” Knock ne yashigo daga k’ofarta. Kafin tace zata bud’e tajiyo muryan Anas “ga luggages naki and ba zama zakiyi cikin d’akin ba am hungry kifito ki dafa min dinner, kinji?” “Naji” tace chan k’asa k’asa. Seda ta tabbata yabar wajen ta bud’o k’ofar tashigo da akwatunan nata tare da ajiyesu wajen ‘yan uwansu. Hijabin jikinta tacire had’e da kayan ta, sannan ta ciro wani silky white fitted doguwar riga me spaghetti hands tasa tare da sake maida hijabin nata. Anan ne ta fito, seda ta tabbata ta rufe kusan rabin fuskarta da hulan hijabin nata sannan ta fara neman hanyan kitchen se addu’a take Allah sa kar su had’u da Anas aiko tana leqa parlour ta gansa zaune kan one seater, vest ne da shorts a jikinsa kad’ai yayi cross legging k’afa. Kafin ta koma baya yaganta “come back” ya fad’i a lokacin da yake ajiye newspaper’n hannunsa a kan side table. Numfashi ta saki sannan ta tako parlourn idanunta matse gam. “Gyara hijabin naki.” Banza dashi tayi, “don’t let me repeat myself.” A hankali ta miyar baya idanunta na a k’asa har yanzu. “Good, so me zaki dafa mana.” “Nima bansani, tell me what you want.” “Just cook anything yummy good. I hope kin iya girki banason jagwal-gwale.” lallai ma tace a ranta. “Yes...? Kin iya?” Kai kawai ta gyad’a masa seda ta juya ta soma tafiya yasake kiran sunan ta kamar wacce zatayi kuka ta juyo. “Cire hijabin, ko bakisan ba’a shiga kitchen da hijabi ba? Ba fata ba what if mistakenly hijabin naki yakama da wuta fah? Kicire.” Ba k’arya a maganansa dankuwa ko Mami ta hanata shiga kitchen da hijabi hannu tasa zata cire sekuma ta tuna kayan dake jikinta ai seta miyar da hannun nata baya. “Cire hijabin ne baki iya ba?” “Na iya excuse me inje d’aki incire.” nan ta juya. “Not excused, dawo kicire anan Fannah banason surutu.” “But Anas-” “But Anas what?” Ya katse ta. “Mene a jikin naki ban gani ba” se yad’an tsaya ya murmusa, baki ta murgud’a masa ganin bai kallonta. The moment ya sake d’ago idanunsa ya aza akanta kuwa seta kawar da kanta “just take it off before I lose my temper.” “Anas ai zan cire amman ka bari inje d’aki mana ko anan zan ajiye?” “Eh anan zaki cire kuma ki ajiye, I’m hungry kina b’ata min kokaci.” Zata sake magana ya daka mata tsawa “Now!!” Bata san seda ta cire ba se b’ari take. Mak’ale hijabin tayi a k’irjinta da hannayenta bibbiyu akai se kallon gefe da gefe take tana b’ari. Wai ita da ace atamfa ne a jikinta da barata damu ba amman wannan shegen kayan datasa dan shan iskan ne ke damunta. “Oya ajiye ki bani waje.” Fuska ta maraice “Anas kayan jikin nawa ne... Erm... Erm...” Yi yayi kamar ze nufi wajenta atake ta ajiye hijabin kan kujera. Murmushi ya saki tare da sake daidaita zamansa cikin kujeran. Kallo ya k’are mata up-to-down anan ne ya gano dalilin da batason cire hijabin. Hannu tasa ta soma kare k’irjinta ganin haka ya mata nuni da hannu da nufin ta basa waje “go am not interested” yace da ita chan k’asa k’asa kuwa ba abinda yakeso kaman kallon jikin Fannah. Juyawa tayi ta soma tafiya. Bin bayan ta yake da kallo yana murmusawa abinsa. Se anan ta tuna kayan jikinta silky ne showing komai yake gashi batasa underwear skirt ta ciki ba, kayan nata ta soma ja tana kare bayanta, ahaka harta fice daga ganinsa. Murmushi kawai yake, leb’b’an k’asan sa ya cize tare da d’ago newspaper’n dan cigaba da karantawa sede sam yakasa dena tunanin Fannah. _50 minutes later..._ Rik’e Fannah ke da wani had’ad’d’en food warmer a hannunta ta lab’e jikin k’ofar kitchen d’in tarasa ya zata k’ariso gaban dining table ta ajiye, ganin ba Ubangiji se Allah kawai tasa kai ta ajiye idanun Anas na akanta. Bayan ‘yan mintuna ta gama jera kan dining d’in tare da d’iba macaroni da co-slow data girka musu a plate nata. Parlour’n ta k’ariso har a yanzu Anas bebar kallonta ba ignoring nasa kawai tayi. Seda ta d’aga hijabinta da d’ayan hannun ta tace, “dinner is ready.” Daidai ta juya kenan Anas yayi tsalle daga kan kujerar dayake zaune akai se gabanta har tsorata tayi. Plate na hannuntan ya soma amsa, “Anas my plate gachan naka a flask a dining.” “I know” yace da ita tare da amshe hijabin d’ayan hannun nata ya miyar kan kujerar. “Anas hijabi na.” ganin ta mik’a hannu zata d’aga yayi saurin d’agawa yayi wulli dashi achan k’asa yayi decending. Kafin tayi magana ya rik’o hannunta har gaban dining table ya jata. D’aya daga cikin kujerun yaja mata kallonsa ta tsaya yi. Abincin ya ajiye a gabanta sannan yace, “sit.” “But-” “Anan zakici so sit banason surutu.” Badan tanaso ba ta zauna yaja mata kujerar ciki. Opposite da ita ya zauna shima. “Serve me.” Kai ta d’ago tana kallonsa lallai ma Anas, ayi masa girki akawo masa, zubawa ma yace se anyi masa? Sauran chi ma kace ni zanbaka. Katse mata tunani yayi “well? I’m hungry.” “Toh Anas barin d’auko hijabi na please.” “Fannah I like you this way, the only time zakisa hijabi is in zamu fita ko munyi bak’i but in ni da ke ne banaso, kinji?” “Naji amma-” “Chapter closed” ya katse ta. “Now serve me dinner.” Mik’ewa tayi duk she is feeling uncomfortable ta bud’e flask d’in ta zuba masa abincin da co-slow se binta da kallo yake adaidai gabansa ta ajiye tare da tsiyaye masa exoctic juice cikin cup sannan ta koma ta zauna. Spoon d’aya yakai ciki har ya bud’e baki ze fara mata masifa seyaji girkin yayi dad’i komai is perfect, be tab’a cin macaronin daya mai dad’i kamar wannan ba no offense amman Fannah tama fi Ummie iya girki. Wasu biyun ya k’ara kaiwa cikinsa itade Fannah kallonsa kawai take. “Anas bakace komai ba” ta fad’a kanta a sunkuye. “Me kikeson inche? Maggi yayi yawa kokuma gishiri?” Gira ta had’e takai spoon d’aya baki itama sekuma taji komai yafita daidai. “Amman Anas ba abinda yayi yawa fa, zak’in is okay.” “Toh ni bemin dad’i ba, ahaka ne kin iya girkin? Dan de inajin yunwa ne kawai zanchi mschw!” yaja ‘yar k’aramar tsuka. Haka yata loda abincin ita de Fannah na ta ido ne. Mutumin dayace abinci beyi dad’i ba amman yafita chi. Bayan daya k’are plate nasa ya sake dad’awa. Baki tabud’e sosai tana kallonsa. “I thought kace beyi dad’i ba kuma nga harda k’ari kayi.” “Nayi ina ruwanki? Yunwa nakeji is not as if kin iya girki.” Murmushi kad’an ta saki danko tasan he don’t mean what he said. Bayan da suka gama chi ta kimtsa wajen. Sallan isha ya jasu. Bayan nan takoma d’aki tasoma tsefe kitson da Afrah ta mata last 2 weeks. Guda uku kacal tayi tasoma jin tsoron zama a d’akin ita kad’ai, ina ma ace gidan da hayaniya amman sekace mak’abarta shiru. Fitowa parlour tayi ta tsinci Anas zaune kan kujera yana kallon football. Kamar ance Anas juyo ya juya idanunsa basu sauk’a a ko ina ba sekan Fannah dake tsaye da kayan jikinta na d’azu. Kai ta kawar ta tako a hankali ta zauna kan d’aya daga cikin kujerun ta cigaba da tsifarta. Bayan daya k’are mata kallo ya miyar da kallonsa kan TV’n lokaci zuwa lokaci yake satan kallon Fannah, da ta tsefe biyu se ta tsaya taja hannunta normally agida daman ko Mami ko Afrah ke taya ta, dama dama ache kalaba ne takan iyawa da kanta. “Come let me help you” yace da ita. Kai ta d’ago cike da mamaki tana kallonsa. “Eh?” Ta tambayesa fuskarta cike da neman k’arin bayani. Hannu ya nuna mata “come.” “Erm Anas don’t worry thanks zan iya da kaija.” “Baraki iya ba wannan uban gashin kin just come.” Tunanin taje ko a’a karta je take ganin haka ya taso daga mazauninsa ya dawo kan kujerarta. Baya ta matsa da wuri sede kafin tayi hakan ya cafko hannunta tare da karb’e kibiyan. Ta bud’e baki zatayi magana ya kwantar da kanta kan cinyarsa. Wani irin baqon yanayi ta tsinci kanta ciki. “Anas zan zauna a k’asa kar cinyoyonka su maka tsami.” “Dake ance miki rago ne ni ai.” Shiru tayi bata ce komai ba a hankali taji yasoma tsefe mata kitson. Sake jikinta tayi sannan tace, “thank you.” Yi yayi kamar be jita ba, ”Anas I said thank you.” “No big deal.” Haka yata tsefe mata kitson har yayi rabi saura rabi wanda seta juya tana fuskantanshi ze iya tsefe mata. “Fannah turn around.” Shiru beji amsar taba. “Ke Fannah!” Fuskarta ya leqa yaga bacci ma take mekyau, lallai ma yace a ransa yana murmushi wato dan dad’in tsifar har tayi bacci. Juyo da ita yayi gabad’ai sannan ya cigaba da mata tsifan. Yanayi yana kallon fuskarta cikin baccin tace, “taya ka iya tsifa haka? Kafi Afrah ma iyawa.” Murmushi kad’an ya saki be amsata ba chan ta sake cewa “haka kitso ma ka iya, god bless you Mr. Fauzi.” Dariya kad’an yasaki wanda ya k’ara masa kyau seda ya gama ya kama mata gashin gu d’aya tare da d’aga ta ya kaita d’akinta ya kwantar da ita ya rufeta da bargo sannan ya kashe wutar d’akin ya rufo mata k’ofar. D’akinsa ya nufa ya kwanta shima. _2 hours later..._ Firgit Fannah ta tashi daga bacci around 11:30PM ganin ta soma mafarke mafarken nata, hamdala ta saki ganin mafarkin beyi nisa ba. Gefenta ta tab’a taji wayam ba Anas. “Anas!” Ta kira sunansa, a 360 ta janyo pillonta da bargo tabar d’akin. Ta bud’e nan ta bud’e chan har ta isa d’akin Anas gwada bud’ewa tayi taji a rufe. Knocking take bam-bam. Cikin bacci yace, “who is it?” Hamdala ta saki jin muryarsa. “Anas please let me in Fannah ce.” “Bakiyi bacci ba dama?” “Anas dan Allah ka bud’e.” A kasalnce ya mik’e ya bud’e mata, kallonta ya tsaya yi “what now?” “Anas mutumin” ta sanar dashi a kidime “Muje in rakaki ki kwanta toh.” Kai ta kad’a “please lets sleep together.” Abinda yakeson ji kenan dama. “Kaifa kace d’azu ka yarda zamuna kwana tare.” “Noo Fannah ba abinda nace ba kenan ce miki nayi naji I’ll think about it.” “Eh toh ni whatever please let me in.” Kafad’a ya buga mata. “Anas please...” Ta maraice fuska tana k’ok’arin k’irk’iro hawaye. “Okay naji shigo” ya matsa mata. Cike da murna tashiga kan gadonsa ta haye. “No! No! No! No way sauk’a min akan gado, ke baki iya bak’wanta bane? Kin wani zo kin hayemin kan gado, off my bed.” Cike da kunya ta sauk’o tana tattara pillonta da bargo. “Kin manta me kikace d’azu? Cemin kikayi ko a k’asa ne zaki kwana ko ba haka ba?” “Eh Anas but-” nan ya katse ta ta hanyan aza yatsansa bisa lips nasa. “Shh! so a k’asan zaki kwana.” “Ayyah Anas mana...” “Oya zo ki koma d’akin ki.” Da wurwuri tace, “a’a na yarda zan kwanta a k’asan.” “Good” yace yana murmusawa. Wani babban bargo ya ciro ya mik’a mata “gashi shimfid’a achan” yamata nuni da hannu “ki kwanta in kin gama ki kashe min wuta” yana kaiwa nan ya haye gado. D’agawa tayi ta shimfid’a kusa da gefen gadonsa dan tsoro. A hankali ya bud’e idansa daya rufe “Fannah bafa anan nace ba, achan” ya sake nuna mata da hannu. “Anas I know please let me sleep here chan d’in ina tsoro.” “Whatever” ya miyar mata. Bayan data gama komai ta kashe wuta ta dawo ta kwanta har a yanzun tsoro takeji, be isheta ba seda tajawo kad’an daga bargon da Anas ya ruhu dashi ta rik’e se b’ari take ta kasa komawa bacci. Shima kasa baccin yayi hankalinsa duk na a wajenta. “Fannah” ya kira sunanta a hankali. *beeenovels.blogspot.co.ke* *© MIEMIEBEE* *beeenovels.blogspot.co.ke* [12:57, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 6⃣4⃣ Cikin murya me rawa cike da tsoro ta amasa , “na’am.” “Are you still afraid?” Kai ta gyad’a wane yana kallonta jin shiru ya juyo ya kalleta, ganin hannunta rik’e da blanket nasa ya tabbatar masa tsoro takeji har yanzu. “Come” yace da ita. Abinda take jira dama kenan ba tare da b’ata lokaci ba ta d’ago pillonta ta haye gadon daga chan k’arshe. Matso da pillow nasa yayi kusa da nata. “I’m here kinji?” Yace da ita a lokacin daya aza kanta bisa k’irjnsa. Kai ta gyad’a a hankali tare da zagaye hannunta kan cikinsa, yana shafa bayanta a hankali har tasamu ta koma bacci. _7:00AM_ Yanzu take gama had’a dining table, jin shiru Anas be fito daga d’aki ba har yanzu yasa ta mik’e dan duba ko lafiya, tana bud’e k’ofar Anas na bud’e towel nasa dan gyarawa tun d’azu yak’i shiga wanka se a yanzu ya ke fitowa. Ido wuru-wuru Fannah ta zaro tare da sako baki in shock, sandarewa Anas yayi ya kasa rufe towel nasan. Daga bisani taja k’ofar ta rufe alokacin hankalinsa ya dawo jikinsa ya d’aure towel d’in gam bakamar yadda ya saba yiba sakwa-sakwa. “What just happened?” Ya tambayi kansa disbelievingly. “Did Fannah.... Did Fannah? Oh God! No!” Hannu yasa yana hargitsa gashin kansa tare da jan wani doooogon tsuka. Fannah data sandare har yanzu a bakin k’ofa ta rasa gane ma ko a duniya take ko lahira, kallon k’ofar take har a yanzu baki wangalau har d’igan miyau take. Daga bisani ta kad’a kanta “La ilahi! Ya Salam! Astaghfitullah, Astaghfirullah, Astaghfirullah...” Sede har yanzu bata bar tunanin abinda ta gani ba. “Ya Salam ina Qur’ani inje in karanra.” Daidai zata juya kenan Anas ya bud’o k’ofar d’akinsa kamar ance su kalli juna suka d’ago kai suna kallon juna sun kusan minti suna a haka sannan daga bisani ya kawar da kansa besan meba seya soma jin kunyarta. “Uhm uhm” tayi gyaran murya. “Anas I’m sorry bansan... Bansan” ta tsaya sosa kai. “Is okay kema kin rama now we are even” ya galla mata harara. Tafiya ya soma ya na nufan dining area binsa ta soma tana fad‘in “Anas ba fa ramawa nayi ba, bansan ka bud’e towel naka ba, da ban shi-” bata k’are maganan ba ya juyo yana mata wani irin kallon dayasa hanjin cikinta d’aurewa. Kanta ta sada k’asa tana murza yatsunta “me kika ce?” “Babu nace I’m sorry.” ‘Yar tsuka yaja ya k’arisa kan dining d’in bayansa tabi tayi serving nasa, nan ta d’ibi nata itama ta zauna ganin haka ya mik’e. “Anas ina zakaje?” Be kalleta ba yace, “d’aki.” Hannunsa ta rik’o ta dakatar dashi “wait, mesa?” Idanunsu na had’uwa ya kawar da kansa “sake min hannu unless you want me to be late for work.” “Anas I said I’m sorry nid’in baka kalleni bane...” Sekuma tayi shiru “sit kaji? Lets just assume ban gankan ba, lets all say it never happened okay?” Kai ya gyad’a mata ya nisanta “but the picture of me... Erm it is still stocked in your head, right?” “No nayi deleting babu bangani ba, sit kaji?” Hannun nasa ta sake a hankali ya zauna bayan sun gama ya koma d’aki ya sako suit nasa tare da saqalo jakar laptop nasa, wanka da turare yayi as always sannan yafito alokacin ta koma d’akinta ita kuwa. Har yakai bakin k’ofa sekuma ya dawo ya nufa d’akinta, knocking yayi ta taso ta bud’e masa. Besan me ba seyaji yanason sanar da ita ze fita, “I’ll be going” yace da ita yana kallon k’asa. “Okay Allah ya kare, what will you like for lunch? Oh sorry jiya kace girkin beyi dad’i ba just buy something and eat.” K’ofar ta miyar zata rufe yasa hannu chak ta tsaya. Hannunsa yasa k’ark’ashin hab’anta “Fannah I don’t mean any of those words, I was joking actually you’re the best cook.” Ya k’are maganar yana mata murmushi. Sosai taji dad’i “do you really mean what you said now?” Kai ya gyad’a mata “yes Fannah I do, you are best at cooking.” “Thank you so what will you like to eat today?” “Anything I trust you, I’m going now.” “Okay Allah ya kare.” Har ya juya se ya dawo ya rik’e kanta da hannayensa biyu tare da aza mata hot peck a goshi, wani irin nishi ta saki ta d’ago kai tana kallonsa cike da mamaki, kashe mata ido d’aya yayi (wink) sannan ya sakar mata dawani murmushin daya sosa mata zuciya d’aki ta koma da gudu tare da rufo k’ofar. Kan gado ta fad’a takasa dena murmusawa. “He pecked me! He pecked me! Omg! This can’t be happening” wajen mirror ta nufa tana kallon goshinta daidai inda Anas yayi kissing wani sanyi taji ya ratsa ta se murmusawa take. Kasa riqeta k’afafun nata sukayi ta sulale k’asa sewani blushing take tafi 30minutes ahaka sannan ta tattara kanta tashiga bayi tayi wanka. Shima Anas yana zaune a office amman hankalinsa na akan Fannah he can’t hide it anymore. “Yes I’m in love!” ya fad’a a fili dawani murmushi ta gefe guda a fuskarsa. “Theres no denying again I love Fannah, I’ve said it, I love her and I have to let her know. I don’t know how it all happened but I don’t want her out of my life, zan sameta in mata magana muyi canceling contract marriage d’in I’ve got to tell her I love her.” Daidai nan knock yashigo “come” yace. Kacallah ne ya k’ariso “good morning Sir.” “Morning” yayi greeting nasa back. “Any papers to sign?” “Oh yes, yes Sir” ya amsa tare da gabatar masa da papers d’in bayan da Anas ya gama signin yace; “Erm.. Sir ansamu matsala da wiring na 2nd and 3rd floor electrician namun yakasa gyarawa.” Jira kawai Kacallah yake Anas yace masa ‘kaje kace masa he is fired and find someone better kayi replacing nashi’ to his suprise Anas yace, “kaje kace masa ya sake gwadawa inya kasa anemo external electrician yatayasa su gyara okay?” Baki Kacallah ya bud’e yana ganin ikon Allah, anya kuwa Boss ne? “Kacallah kajini kuwa?” “Yy.. Yes Sir naji, thank you.” “You’re welcome.” “Wow Sir you seem in a good mood today.” Seda yasaki brightest smile nasa sannan yace, “yes I’m happy today Kacallah, kaje kayi ordering friedrice and chiceken from Int’l Hotel for free ma kowani staff anan harda cleaners.” “Wow... Wow thank you so much Sir.” “You’re welcome.” Bayan Kacallah ya fice Anas yayi grabbing pen da paper ya fara had’a name nasa dana Fannah. Sunan Enterprise nasa yakeson canzawa. Yayi ya goge yayi ya goge haka yatayi... _3:40PM_ Aiki sosai Fannah keyi a kitchen yanzu tagama had’a kidney sauce, stew nata ma nan a ajiye ta riga ta gama coconut rice d’in take jira ya nuna ta sauk’e. D’inkin lace ne red and black, riga da skirt sanye ajikinta ya mugun amsar jikinta. Sab’anin kullum yau tad’anyi applying makeup tayi lining tasa mascara ta taje dogayen lashes nata kamar yadda Afrah ta koya mata. Jan janbaki ne mekyau a bakinta sosai tayi kyau, tad’an kitsa calaba k’ananu guda uku tacirosu tagaba wanda tsayinsu ya sauk’a a kasan k’’irjinta da kad’an. Parlour tafito dan shan iska kafin shinkafan ya nuna rurin wayarta yasa ta mik’a hannu ta d’ago daga kan centre table ‘Anas’ taga ke kira. Take taji wani erin farin ciki ya rufeta wanda sakamakon haka yasata murmusawa sosai a nitse ta d’aga tare da komawa kan kujera ta zauna. “Hello...” Tace “Hey Fannah” yace da ita batasan meba amman seji tayi kamar yau ta fara sauraron muryan Anas danko be tab’a mata dad’i haka ba. “Na’am, Anas.” “So what are you doing?” “Nothing just cooking.” “Yummm thats why nakejin k’amshin spices naki har anan.” Dad’i sosai taji se blushing take. “Awwn! Anas don’t flatter me.” “Am serious, yestarday’s dinner was great.” “I hope you enjoy today’s also.” “Ofcourse I will tunda hannayenki ne suka girka.” Kallon hannun nata tayi setaji wani sonsu ya shigeta. “So me kika girka mana?” “Its a suprise, ya office?” Ta canza musu topic d’in. “Boring I miss seeing you over that cushion.” Dariya kad’an tasaki cike da k’asaita. “I miss you shouting at me too, I miss you making me correct 500 papers.” “Oh common Fannah, barin k’ara ba unless ke kikeson kiyi, which I won't let you.” “Mesa?” “Saboda your hand will ache nikuma banaso.” “Ohh really? Ada da kake sani bakasan ze samin ciwon hannu ba kenan.” “Yanzu da da aiba d’aya bane Fannah you know that.” “No I don’t, tell me” ta fad’i tana murmusawa tare da ciza yatsan ta d’aya a hankali. “You used to be my PA but now you’re my wife I... I care about you... Like alot.” Wani irin dad’i taji, ji take kamar an tsunduma ta cikun Al~Jannah. Shiru tayi ta kasa mayar masa da amsa. “Hello Fannah, you there?” “Uhm yes” ta amsa chan k’asa k’asa. “I said I care about you.” So take tace masa she cares about him too amman kunya bare barta ba. “Fannah don’t you care about me too?” Shiru tayi takasa cewa komai. “Toh shikenan am hanging up.” “No don’t” ta hanasa. “I care about you also.” Take ta kashe wayar tare da rungumesa a yayinda shikuma yashiga photos yana viewing pics nata yabi ya k’osa 4:00PM ya buga yaje ya kalli *FLOWER* nsa danko haka yayi re-saving numbanta a wayarsa yanzu. _4:10PM_ Password ya danna k’ofar yayi welcoming nasa. Fannah najin Mr. Fauzi tasoma cin faracunta. “What do I do now?” Ta tambayi kanta. Kwata kwata ta mance ta bar abu kan wuta taje chan tanata waya da Anas ga shinkafan ya k’one yanzu. Daidai ta aza new pot kan tukunya kenan Anas ya dawo. Kafin ta sauk’e pot d’in daga kan gas ta b’oye inaa Anas ya riga yasa kai cikin kitchen d’in. “Hi” ya ce da ita. A kidime ta juyo ta kallesa wani kyau taga ya k’ara mata kamar yadda shima yake kallonta tayi bala’in masa kyau. A hankali ya tako izuwa gabanta. “Oh hi welcome back.” “Thank you, is lunch ready? I’m starving-” ya tsaya yad’an shinshine kitchen d’in “is something burning?” A rikice tace, “no, nothing ka koma parlour and wait for me, lunch will be ready in the next 30 minutes.” Daya karanci fuskarta seya ga kamar tana b’oye masa wani abu. “Fannah are you hiding something?” Ya tambayeta tare da rik’o hannunta yana murzawa a hankali. So take ta masa k’arya amman sam takasa jin hannunsa akan nata. Sad face take wearing. “Anas I’m sorry shinkafan ya k’one, I’m sorry please kabani 30 more minutes zan sake dafa wani.” “Is that why you’re sad?” Kai ta gyad’a a hankali, “I’m sorry.” “Mugani” yace da ita yana k’ok’arin bud’e pot data b’oye a bayanta. “A’a’ah Anas please don’t kaj-” bata k’are maganar ba ya matsar da ita gefe guda kamar doll baby tare da bud’e pot d’in. Murmushi yayi kad’an “wannan ne ya k’onen?” Kai ta gyad’a a hankali nan ma. “We can eat it kinji?” “Anas we can’t ya k’one zan dafa sabo.” “NoFannah karki tak’ura wa kanki kinji? Ina food warmer’n injuye a ciki.” “Anas...” Ta kira sunansa kan wacce zatayi kuka “Trust me, you wasted your time kika dafa I don’t want your sweat to go in vein. So karki damu kinji?” “Thank you” nan ta mik’o masa flask d’in tana ganinsa ya juye ciki ashe ma k’asa k’asan ne kawai ya k’one amman kunsan abinku da shinkafa se an kai baki ake sanin k’onuwansa. Cikin d’an k’ank’anin lokaci tagama shirya musu dining table tare da serving nasu. Kayan jikinsa ya rage yabar shorts da vest zalla. Kallon sauce d’in yake a rayuwa yana k’aunar kidney sauce. “I love this” yace tare da kai spoon d’aya. “Humm yummm delicious.” D’an murmushi ta saki masa inama karyaci shinkafan abinda tace a ranta kenan sabida taji warin k’onuwan dayake, gashi data kai baki har wani d’aci taji. Yana kai shinkafan baki idanun Fannah na akansa tana jiran ganin reaction nasa. Sosai yajiyo d’acin kuma ya damesa amman bayason sa Fannah feeling sad. “Its great, I told you za’a iya chi.” “Anas are you sure? Bakaji d’acin ba?” “Yes Fannah.” Haka yata cin abincin dukda ba dad’insa yake ji ba yaci yakai rabi sannan yace mata ya k’oshi. Dad’i taji sosai be aibanta abincin ba. So yake ya fad’a mata how he feels about her amman kuma baida courage chan ya yanke hukuncin zuwa tonight ze sanar da ita... _9:20PM_ Zaune Anas da Fannah suke a parlour suna kallon wani horror and scary movie THE SCISSORING. Kamar ance dole se Fannah ta kalla duk tabi ta duk’unk’une kanta jikin Anas da an nuno abin tsoro se ta lume jikinta a nasa, shiko kallonta kawai yake yana murmushi. Kallon *FLOWER* yake mata, how they are so delicate and need protection thats why tunba yau ba yake protecting nata. Wani ihu tasaki take Anas ya kashe Cineman. “Mesa ka kashe?” tace alokacin da ta d’ago kanta daga cinyarsa. “Saboda kinajin tsoro.” “But kace fa kanason ka kalla.” “Not anymore since it scares you.” Zata sake magana ya girgiza mata kai. “So wani channel kikeson kalla?” “Zee world!” ta fad’a da sauri ba gardama yasa mata suka soma kalla. Sun kai 30 minutes suna kallon tashan amman Anas be san me akeyi ciki ba, yarasa meke mata dad’i chan yaga tana hawaye. “Fannah are you okay?” Ya d’au ma ko shi ya mata wani abu. Kai ta girgiza masa “kalli fa mahaifinsu za’a kai prison for 25 years kuma bawai wani abu yayi ba sharri aka mai.” Baki ya bud’e yana kallon ikon Allah yau, lallai hawaye yama Fannah yawa. “Fannah yanzu akan TV show kike kuka?” “Anas is so heart touching, Allah sarki!” duk wannan magana da suke bata juyo ta kallesa ba. Shiko bare iya juran ganin *flower* insa tana kuka ba, karap ya kashe TVin gabad’ai. “Anas why? Dan Allah turn it on.” “No meh amfanin kina kallo kina kuka banaso.” “Toh nabari dan Allah ka kunna.” Zeyi magana kenan wayarsa ya soma ruri. Bayan minti d’aya da d’aga wayar yace, “no! Bawani business trip da zanje.” Daga cikin wayar mutumin yace, “please Sir the meeting is worth millions consider this please.” A tsawace yace, “I don’t care barinje ba, mschww!” Karap yayi hanging. Duk yasa Fannah rikicewa ganin yadda idanunsa suka soma canza launi. “Anas¡ ta kira sunansa cikin wani salo tare da dafe kafad’arsa da hannunta tana shafawa a hankali up and down. “Wani abu neh?” “Babu just don’t mind.” “Anas tell me, I’m your wife remember?” Kai ya d’ago yana kallonta murmushi ta saki masa. “Business trip suke son inje.” “And kace musu baraka jeba?” “Yes” ya amsa tare da gyad’a kai. “But why Anas meeting d’in baida amfani ne?” “Yes” ya mata qarya. “Uh-uh tell me the truth.” “Sure yana da relevance kawai baran je bane.” “Anas but why? You have to go” haka tata fad’a masa dad’ad’d’un kalamu tana shafa bayansa a hankali. “Fannah kefa? I can’t leave you alone with your dreams.” “Don’t worry ko Afrah zata zo ta tayani kwana for how many days ne trip d’in?” “5 days” yabata amsa sam be so hakan ba. “Ashe ma ba nisa.” “5 days d’in?” ya zaro blue eyes nasa. Juyowa yayi ya rik’o hannayenta biyu cikin nasa “Fannah I’m afraid, I will miss you” yace da ita sincerely daga k’asan zuciyarsa... *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:57, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 6⃣5⃣ Kasa furta koda ‘A’ bakinta yayi she actually can’t believe what is happening. Those this mean Anas na sonta? What if yes? Zata iya son sa itama? Kai ta girgiza I can’t tace a ranta koda kuwa inasonsa I can’t saboda banida martaba Anas ze gujeni duk lokacin daya gano hakan. “Fannah” yakira sunanta cikin wani irin salo yana murza hannayenta da nasa. “I don’t want to leave you.” Murmushi ta k’irk’iro masa “you have to Anas, karka damu we will aways stay in touch ta waya.” Kai ya girgiza mata “waya is not enough saboda I can’t look at your face.” “Thank goodness akoi video calls ko ba haka ba? Kaga se munayi, you have to go Anas for the future of your company kaji?” ta k’are maganar da hannunta cikin gashin kansa. Kai ya gyad’a. “Good so yaushe ne tafiyan?” “Fannah I wanted to tell you this, I have been keeping it a secret but not anymore I’ve got to tell you, ina fatan bare baki tsoro ba and you won’t freak out.” Cike da rashin fahimta tace, “me kenan Anas?” Seya bud’e baki ze fad’a how he feels about her seya kasa yayi hakan sau uku amman ya kasa daga k’arshe ya yanke hukuncin seya dawo daga business trip d’in ze sanar da ita abinda ke zuciyarsa. “Anas kayi shiru.” ta fad’i tare da sauk’e hannunta daga gashinsa ta rik’o hannunsa instead. “What I meant to say is that kinyi kyau yau, you are looking extraordinary beautiful.” Qasaitaccen murmushi sosai ta saki cike da rigima. “Thank you shine abinda kake tunanin ze bani tsoro?” Kai ya gyad’a “well thank you you are looking handsome as always so nace yaushe ne tafiyan?” “I don’t know ban tambayesa ba.” Hannunta ta raba da nasa ta d’ago wayarsa ta miqa mai. “Gashi call him back.” Ba musu ya kira mutumin yamai bayanin komai bayan daya gama yace da ita “tomorrow 7:30AM flight d’in ze tashi.” “Wow! Toh a ina ne business trip d’in?” “A Ukraine ne chan Asia, Fannah its too far I don’t want to go.” Ya fad’i kaman d’an yaro. “Anas hak’uri zakayi, you’re a Man! So man up! Muje mu had’a maka akwatin tafiyan ka.” Nan ta mik’e Anas kam nanan a zaune hannunsa ta ja “lets go” nan ma yak’i motsawa “Anas stand up nowwww.” Kai ya kad’a yana murmusawa. “Ohh!” Ta fad’a tana murmushin itama “kad’au barin iya janka bane?” Signal ya mata da gira yana nuna mata muscle nasa. “Well lets see.” Hannun nasa take ja da iya k’arfin da Allah ya bata dan jawo Anas amman takasa ko motsawa baiyi yadda ya zauna kamar gunki baiko motsi. Har gumi tasoma had’awa ganin barata iya ba ya mik’e da kanshi a dalilin haka ta fad’o jikin shi ba control. Tsayuwa sukayi suna kallon juna na kusan minti uku sannan Fannah tayi gyaran murya “uhm-uhm I’m sorry” ta gwada mik’ewa kenan yamata pressing peck a kumatu. Wani irin electric sparks taji na bin jikinta she can’t help but blush. Ganin d’an kiss daya bata had an effect on her ha murmusa “lets go” yace da ita tare da rik’o hannunta ahaka suka k’arisa d’akinsa. Wardrobe nasa ta bud’e ta b’angaren suits ta soma cirosu. Colour combination masu kyau ta riga had’a masa yana zaune kan gado yana kallonta bayan nan ta had’o masa underwears(vest, boxers and shorts) nasa cikin awa akwatin tafiyan sa is ready. “Mr. Fauzi komi da kake buk’ata na nan.” Kallonta yake yama kasa magana, she is damn cute abinda yake ta fad’a a ransa kenan. “Mr. Fauzi?” Tayi waving hannunta a fuskarsa. Anan ne hankalinsa ya dawo jikinsa. “Yes Fannah what is it?” “Nace akwatinka is ready. Tunanin me kake?” “Ohh thank you babu.” Chan k’asa k’asa tace, “yau wata rana Mr. Fauzi anyi godiya bada wata manufa ba.” “Kinsan naji ki ko?” Mik’ewa yayi dan cafko ta ayayinda ta sa gudu sede kafin takai bakin k’ofa yakama hannunta yadawo da ita d’akin. Kan gado ya fad’a ya kwantar da ita a jikinsa. Data gwada yunk’urin tashi ya hanata. “I’ll be travelling tomorrow Fannah let me hold you kinji?” Kai ta gyad’a a hankali. Bayanta yake shafawa a hankali a yayinda ta zagaye hannunta kan cikinsa. “So kika ce Afrah zatazo taya ki kwana?” “Yes.” “Okay, zanyi hiring like 5 soldiers suyi muku gadi ko sun kasa?” “Har 5 Anas? We don’t need koda one ma we will be fine.” “No Fannah I need to protect you. 5 female soldiers.” “Toh ai mata kaman mu ne ba gara maza bama.” “Banason mazan daga yadda yake magana za’a san kishi ya k’osa. Mesa? Ta tambayesa tare da d’ago kanta tana kallonsa. Kallon nata yake shima “sabida sun fiye sa ido banason su kalla min ke and you too Fannah da zaran zaku fita keda Afrah make sure kinsa hijab kinji? I will talk to my driver shi zena kaiku duk inda zakuje.” “Okay” tace tare da miyar da kanta k’irjinsa. “Look up at me” ya buk’ace ta ba musu ta d’ago kanta. “Promise me bara ki fita ba hijabi ba.” “Anas I promise.” Haka suka yita hira har zuwa 11:30PM sannan suka canza kayansu zuwa na bacci suka koma suka kwanta manne da juna. ***** 6:45AM Tsaye Fannah da Anas suke a bakin k’ofar su, hijabi ne bak’i har k’asa a jikinta saboda presence na driver. Bayan ya k’ariso wajen nasu yace, “Sir everything is in place we need to go now.” Banza dashi Anas yayi kwata kwata bayason tafiyar Fannah ce tace, “okay yanzu zezo ka jirasa a mota” bayan ficewan driver ta rik’o hannayensa cikin nata. “Anas you need to go kaji? Yi hak’uri.” “I don’t want to miss you” ya fad’a sincerely. “We will keep in touch kabar damuwa please ba haka nasan Mr. Fauzi ba, the Mr. Fauzi I know is a Boss!” K’arfin guiwa kad’an yaji yasamu “okay ina isa chan zan sayi new sim and call you kinji?” Ta gyad’a kai. “Fannah as I told you duk inda zakije kisa hijab and call me ki fad’a min in zaku fita kinji?” “Yes Sir” ta gyad’a kai. “Neman tsokona na kike koh?” “No Sir” hannunsa ya raba da nata yad’an mata chakulkuli. Dariya sosai take haka shima. “Okay Anas you need to go driver na jiranka. Allah dawo da kai lafiya yakuma bada sa’a” tace tana gyara masa necktie nasa. “Ameen” yace yana binta da kallo. “Wishing you all the very best of luck safest trip Anas my hubby.” “Thank you my wifey” ya amsa. “Up you go, bye” daidai ta juya kenan ya rik’o hannunta ya tsayar da ita. Fuskarta yayi cubbing da hannayensa bibbiyu tare da manna mata hot peck a goshi sannan a kumatun ta na dama se ana hagu se k’arshe akan tip na hancinta. Da fuskar mutum na dawo da ja dan blushing dana Fannah yayi dan kuwa she can’t help but blush ga wani kunya dataji ya ratsa ta, ta kasa koda d’ago kai ta kallesa. Da yatsan sa k’ark’ashin hab’anta ya d’ago fuskarta da k’yar ta iya ta aza idanunta akan nasa. “Keep yourself for me and you, okay?” Kai ta gyad’a “I will surely miss you.” Baki na rawa tace, “I will miss you too” duk setaji batada k’arfi sakamakon kisses da Anas yayi mata a fuska. Bata san meh ba setaji batason ya tafi itake tilasta masa seya tafi but not anymore. Tasan inda zata k’ara minti d’aya tsaye anan zatayi kuka. Ciki ta koma da wuri ta rufo k’ofar “wait!” yace amman ko sauraronsa batai ba. Hawaye taji suna sauk’o mata kan kumatu wanda batasan dalili ba. Hannunsa ya jingina jikin k’ofar a hankali ya furta *“I love you my flower”* _10:40AM_ Afrah ne tsaye bakin k’ofar su Fannah yanzu driver ya ajiye ta se kashe selfie take wajen k’ofar. Bada dad’ewa ba Fannah tazo ta bud’e mata. Tana tako k’afarta k’ofar yayi kukan “unknown welcomed.” “Ya Fannah magana fa k’ofar yake.” “Kinzo kisoma cikani da surutai ko?” Sunan Afrah tayi registering jikin k’ofar kamar yadda taga Anas yayi ranan. “Afrah added to family list, welcome home Afrah.” k’ofar yace. “Wallahi ya kira suna na, thank you” ta fad’i tana tsalle. Da idanunta suka had’u dana Fannah kuwa seta gano yarta tayi kuka danko tun tafiyar Anas take kuka se ayanzu tayi shiru. “Ya Fannah bade kuka kikayi sabida tafiyan Ya Anas ba? Hehe soyayya ruwan zuma. Kodan hawayen da kika zubar ma dole ya dawo miki karki damu ni ba wannan ba zo ki zagaya dani inga wannan uban mansion nakun. Kinsan da driver ya dosa gate na gidan nan cewa nayi a raina shikenan ze kawo ni gidan gintile kai saboda had’eyewar gidan. Chap! Thank god nazo da kayaki turum insamu in kakkashe-” bata k’arisa maganar ba idanunta suka sauk’a akan Cinema dake parlour. “La haula! Fi sha’tillahi! Ya Fannah! me wannan?” jakarta ta ajiye ta nufa wajen tana shafawa tana gwada tsayinta da Cineman. “Karki fad’amin TV ne wannan daya kusan yina a tsayi.” “Mschw! ke kinma fini k’auyanci wallahi ba TV ba sunansa Cinema mumu.” Cewar Fannah nan Afrah ta ciro wayarta ta kashe selfies a wajen haka tata zuba k’auyanci kan ba gobe. Ba inda bata shiga ba a gidan har wanka tayi cikin jacuzzi. Data shiga b’angaren store rooms kam seda ta b’ata waya tama Fannah tazo ta fidda ita. ***** Tun 9:00PM Fannah ke jiran call daga Anas hankalinta duk yabi ya tashi Afrah kam na chan a parlour tana kallo. Alwala ta d’auro tayi nafila raka’a hud’u tana rok’an Allah kare mata Anas. Yadda Fannah taga rana haka taga dare sam ta kasa bacci se da Asubah around 5:14AM taga international number na kiranta ba makawa ta d’aga. “Hello Anas” tace murya cike da tashin hankali. “Fannah bakiyi bacci bah?” “Banyi ba na kasa Anas, I was worried sick about you.” Dad’i sosai yaji jin she cares about him. “I’m sorry nima bamu jima da landing ba.” “Toh ya gajiya?” “Gajiya akoi sosai, joints d’ina duk sunyi tsami.” “Ayyah sannu if only I was there in maka tausa.” “Don’t worry kinyi mafarkin mutumin yau?” “A’a banyi ba...” Haka suka ta hira se chan ta rok’esa da ya kashe wayar ya ajiye ya huta. Badan yanasi ba yace; “Okay, I miss you.” “I miss you too” take tayi hanging. Afrah mumafuka ashe ba bacci take ba kamar aljanah ta zauna seda ta razana Fannah. “Wai dama ba bacci kike ba?” “Ana hiran soyayya ina zan iya bacci?” **** Tun tafiyar Anas kullum suna kan video call kokuma voice call da Fannah they are both missing each other sosai. Yasa an masa rescheduling meetings nasa in 3 days ze gama da daren ranan ya hau jirgi in the 4th day ya iso Nigeria in shaa Allah he is missing Fannah much da bare iya juran har kwana biyar ko shida be tab’a jikinta ba. As a suprise yakeson yazo mata sesa yak’i sanar da ita. So d’aya su Amal da Shettima da Aiman duk sukazo sukata having fun har kamar k’aramar party suka maida had’uwan nasu. Shettima shima Anas ya tusa sa cikin business nasu Kashim yana samu sosai yanzu yabar sata. **** A yau Anas ze bar Ukraine. Tun da Azahar Fannah ke trying layinsa wai switched off tayi har tagaji koda Asuba ma data gwada still switched off hankalinta yayi matuk’ar tashi toh meke faruwa? Da k’yar tasamu tayi wanka dukda Afrah na kwantar mata da hankali amman ina takasa samun sukuni. Da Azahar Afrah taci kwalyanta ta fice yawo ya rage Fannah kad’ai a gida. Zaune take a parlour, wani farin dogon riga ne meh spaghetti hands da jikin roba a jikinta ta had’a gashinta a tsakiyan kai ta kama tabar jelan na yawo ko powder babu a fuskarta duk ta tattara hankalinta ta baiwa wayarta tana jira ko Anas ze kirata. K’aran shigowar text wayarta yayi da hanzari ta duba taga new line da batasani ba. _Open the door_ taga, kanta ne ya d’aure kode Afrah che tayi new line bata damu dasa ko hijabi ba ta taso ta bud’e. Kasa yadda da abinda idanunta ke gane mata tayi. “Anas?” Ta kira sunansa cike da rashin yarda “Anas is this you?” ta tambayesa Murmushi ne fal d’auke a kyakkyawar fuskarsa hannunta yaja seda ta fad’a a jikinsa. Hugging nata yayi gagam wane za’a k’wace masa ita. “Fannah I missed you, I missed you so very much that I had to reschedule my meetings just so as to be with you.” Ya fad’a bakinsa manne da gefen wuyanta yana shinshuna daddad’an k’amshin jikinta. Sandarewa tayi a wajen jin jikin Anas akan nata, jin yadda ya matseta ajikinsa, a hankali ta d’ago hannayenta ta zagaye su jikinsa itama tare da sake lume jikinta a nasa. “I missed you too Anas, I missed you alot, nad’au wani abu ne ya sameka tun jiya nake trying number’nka switched off hankali na ya matuk’ar tashi” ta k’are maganar cikin sautin kuka da hanzari ya raba hug d’in tare da sa hannu ya share mata hawayen. “Shhh! *Flower* please don’t cry kinji? Banyi haka dan in saki cikin damuwa ba I thought I might suprise you I’m sorry.” Sake hugging nasa tayi gagam ba k’arya tayi missing jikinsa me uban k’amshi dakuma d’umi kamar yadda shima yayi missing nata jikin. Sunfi minti biyu suna manne da juna sannan ta sakosa tare da rik’o hannunsa “come in” daidai kan kujer ta zaunar dashi. “Bansan yau zakazo ba gashi ban dafa komai ba. Let me get you koda indomie ne.” Hannunta ya rik’o “no don’t bother banajin yunwa, ganin ki kad’ai ya warkar min da yunwa na.” Janta yayi ta fad’a kan cinyarsa. Hannayenta ta zagaye a wuyansa a yayinda ya zagaye nasa a ‘yar kunkuminta. Kallom cikin idanun juna suke daga bisani Anas yafara magana da cewa; _“Fannah I don’t think I can hide it anymore, am tired of playing the game, I wanted keeping it as a secret but not anymore ‘cause its killing me. A da ban tab’a kawowa a raina I will ever love a woman ba, duk ‘yan matan danayi a baya badan inasonsu bane nayi dating nasu ne saboda inyi breaking hearts nasu kamar yadda suma suke dating d’ina saboda am rich and handsome they are either after my looks or money but Fannah when it comes you ke ta daban ce. You are different, unique in your own ways. Baki damu da material things ba, you are not mesmerized by my handsome face. Munyi aure inform of contract, nace miki karkiyi falling min and bakiyi ba, you obeyed the rule but me? I didn’t Fannah, I broke the rule because I’ve fallen for YOU. Fannah bansan ya akayi duk wannan abubuwa suka faru ba all I know is that I want you by myside forever, I don’t wanna loose you da zaran na nisanta dake koda na ‘yan seconds ne ji nake kamar shekara da shekaru ne. I love your attitude, personality, charimsa, knowledge, voice, smile, hair, body, I love every single thing about you and most of all I LOVE YOU FANNAH, FANNAH ALEEYU I LOVE YOU, I will never want to lose you. You are like a flower in my life who shines brighter tha the sun. You brought back my joy, made me religious, kin kyautata alak’a na da mahalicci na, shed away my fear and sorrow, made me into the man I am today, I don’t drink anymore, bana wasa da Sallah hasali ma kyautata sa nakeyi yanzu, duk wani abinda haramun ne ina k’ok’arin kiyayewa, things that I don’t like I LOVE yanzu. Fannah like how flowers shine and outbright places haka kike a rayuwa na I’m lost without you. Funny how I’d fall in love but believe it or not I love you Fannah and I didn’t say it saboda kice min you love me too. I said it because I need you to hear it I love you flower and I want you to stay with me forever..._ ya k’are maganar tare da sake matse ta ajikinsa. *© miemiebee* beeenovels.blog.spot.co.ke [12:57, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 6⃣6⃣ Mutuwan zaune Fannah tayi bata tab’a tsammanin jin wad’annan dad’ad’d’un kalamu daga bakin ANAS IBRHAIM FAUZI ba, a rayuwa bata tab’a sanin Anas nada sweet side haka ba, shin dama ya san kalamun soyayya haka? bata tab’a kawo wa aranta Anas zeso talaka kamar taba, last dataga picturen budurwarsa model ce irin wanda akesa hotunansu jikin kwalin relaxer ko attarchment d’innan. Me Anas zeyi da ita? Me take dashi? Does he really meant all that he said? Is it true that kamar yadda tajima da kamuwa da sonsa shima haka ya kamu da sonta? What now yanzu? Meyake nufi dayace he wants me to stay in his life forever? So yake muyi cancelling contract marriage d’in? Toh ai nima abinda nakeso kenan sede da akwai matsala, I can’t do this banida martaba. Aduk lokacin da Anas ya gano hakan ze nisanta daga gareni, zece naci amanarsa ban sanar dashi ba. Wata zuciyar ce tace mata toh ai seki fad’a masa. A’a I can’t, I can’t tell him ze gujeni I love him, I love Anas also but I can’t express my feelings for him even if I want to I can’t. Hannunta dake zagaye a wuyansa ya zaro d’aya tare da had’awa da nasa. “Fannah why are you silent?” Ya nisanta _“now I get it, I’ve been a monster to you Fannah tun rananda muka fara had’uwa dake nasoma k’untata miki, I made you passed through alot of horrible past and I do regret each and every of that, inda zan iya jawo time d’in baya da nayi so as to make you happy. Fannah I’m so sorry kinji? Please don’t punish me akan past d’ina I’m not who I used to be Fannah, you changed me. Kiyi hak’uri kiyafemin duk abinda na miki please nayi sune bisa rashin sani, I was stupid to make you correct 500 papers, stupid to always make you cry, stupid to make you copy down non-important mails, amman ki yarda dani hakan duk ya faru ne because I love you. Tun alokacin dana gano ina sonki naji I couldn’t accept it and thats why na riga punishing naki but now I do Fannah, I’ve acccepted my feelings for you. I’m so so sorry its never to late to say sorry, kiyafemun kinji? Please...”_ ya k’are maganar da kansa na kallon k’asa. Kwata kwata batasan me zata fad’a masa ba, he made her speechless, shin ina girman kan Mr. Fauzi? Anya kuwa wannan ne Mr. Fauzi data sani? Wanda ba ya iya furta sorry da please se in takama. A zahirin gaskiya tana sonsa itama saboda aduk fad’in duniya bataga macen da zata k’i na miji kamar Anas ba. Sede batta tsammanin zata iya fad’a masa. Hugging nasa kawai tayi ta matse sa kam a jikinta, wannan rana ya kasance babbar rana a rayuwarta wanda barata tab’a iya mancewa dashi ba. “Anas you don’t have to be sorry” ta fad’a cikin wuyanshi “ni baka min komai ba so stop apologising, mutane nene mu we all make mistakes” seta bud’e baki dan fad’a masa tana sonsa sekuma ta kasa, tayi tayi amman takasa batada courage, tsoro bare barta ba. A hankali ya raba jikinsa da nata thank you *“flower* thank you so much. So does this mean zaki zauna dani? Bara ki tafi kibarni ba?” Kai ta gyad’a masa a hankali. Hannunsa ta aza kan fuskarsa tana shafawa a hankali. “I will never leave you Anas *_INA TARE DA KAI”_* hannunsa shima ya aza kan hannunta dake a fuskarsa. _*“Flower* marriage is not a contract its a feeling a mutual one, muyi cancelling contract marriage d’in kinji? Na duba google earlier na karanta that irin auren contract d’innan ma haramun ne Allah yayi hani dashi kinga kar Allah yayi fushi damu lets cancel it kinji? I don’t want you to leave I want you to stay please.”_ “ you are absolutely right Anas nima seda ga baya nake tuno hadisin don’t worry *_INA TARE DA KAI_* I won’t leave your side kaji?” Kai ya gyad’a “so kin yarda muyi cancelling contract marriage d’in?” “Na yarda lets cancel it” Ya Salam! Ta furta a ranta, ita kanta bata san seda ta fad’a hakan ba yanzu me zatace inya nemi had’a kwanciya da ita? Although Mami ta sha fad’a mata ba dole ne agane she is not a virgin saboda ta juma da sake had’ewa da irin magunan da Mami ke bata sede dan jinin da ake fad’i ana gani wanda akoi matan da ba’a gani daga garesu kuma bawai hakan na meaning ba virgins bane su, so ta kwantar da hankalinta amman ina Fannah tariga tasa aranta tayi believing duk namijin daya kwanta da ita ze gane. Hugging nata ya kuma yi “thank you *flower* thank you so much.” Sosai yaji dad’i sede he is sad bata fad’a masa how she feels towards him ba, but still tace barata barshi ba *_TANA TARE DA SHI_* wannan kad’ai ya ishesa. A nitse ta mik’e daga kan cinyarsa. “So me zakaci in dafa maka, banason ka zauna da yunwa.” Mik’ewan shima yayi, tare da rik’o hannunta “lets go out and eat together okay?” “Bakason in maka girki?” “Banason kisha wahala lets go kinji?” Kai ta gyad’a masa. Bak’in hijabinta ya d’auko yasa mata da kansa seda sukazo fita ta tuna da Afrah. “Anas what of Afrah? Karta dawo ba kowa a gida.” “Tunda na dawo I think it will be better ta koma gida koh?” “Eh I think so too.” “Okay karki damu zan ma driver magana ahaka suka fice.” ***** Bayan La’asar suka dawo alokacin har driver ya maida Afrah gida. Alwala sukayi suka idar da sallah jikinsa ya jawo ta tare da kwantar da kanta a k’irjinsa yana wasa da siraran yatsunta. “Anas” ta kira sunansa. “Yes *flower* ” ya amsa “Why do you call me flower?” Ta tambayesa tare da d’ago kai tana kallonsa. Murmushi ya mata “because you’re small” katse sa tayi “Anas I’m not small, ina fa da tsayi sede kawai I’m slim.” “A ganga da na you are small Fannah, you’re like a baby I can hold in my hands ko barin iya ba?” Murmushi kad’an ta saki “zaka iya.” “I call you flower because you are beautiful kamar yadda flowers suke, you always smell good kullum kina cikin k’amshi like how flowers are, I always protect you and I will also in the future because you’re so delicate like flowers, you are like a star in my life, kin kawo haske a rayuwa na Fannah just as how flowers suke haskaka waje. I cherish you my flower” ya manna mata peck a kai. Dad’i sosai taji ta sake lume jikinta cikin nasa. _Washegari... 6:00AM_ “Anas ka tashi kaji? Akwai office fah.” “Barin jeba I’m the CEO” yace cikin bacci tare da sake jan ta ta fad’a jikinsa. “Mr. CEO kamar ya baraka jeba? Yi hak’uri ka tashi please kaji hubby-wubby yi hak’uri Mr. billonaire.” Idanunsa ya bud’e a hankali ya sauk’esu kan Fannah data sha kwalya da wata arabian doguwar riga purple ajikinta yasha stones. “Yaushe kikayi wanka?” Abinda ya tambaya kenan cike da mamaki. “Ba tun d’azu nake ta da kai ba kak’i up you go please kaga har 6:05AM yayi yi hak’uri” haka da lallab’a ta turasa bayi sannan ta fice kitchen ta had’a musu breakfast. Suna hira har suka gama breakfast nasu cikin kwanciyan hankali. Tayasa tayi ya gama shiri seda suka kai har bakin k’ofa sannan ta tuna da lunch data had’a masa. “I’m coming” tace bayan minti d’aya ta dawo. “Whats this?” ya tambayeta fuskarsa d’auke da neman k’arin bayani. “I made you lunch ko baka so?” “Taya barinso ba Flower?” Ya karb’a tare da bud’ewa favorite nasa yaga ciki. “Ohh! thank you” ya manna mata peck a goshi. “You’re welcome, so take care okay?” “I will for you, my flower.” Fuskarta ta rufe da hannayenta cike da kunya, bayan ya fice ta rufo k’ofar ta koma d’aki tad’an kimtsa kafin masu aiki suzo. Kafin Anas ya dawo daga office tariga tagama had’a musu lunch tasake wanka ta canza kaya. Da tafiyarsa office sau biyu suke video call da voice call d’aya. Anas na a meeting amman yana chatting da Fannah. “Uh Mr. Fauzi you haven’t been participating in today’s meeting” cewar wani d’an dattijo yana sanye cikin black suit. Wayar nasa ya b’oye k’ark’ashin table d’in “I’m sorry what did you say?” “Mr. Fauzi are you okay?” Ya sake tambaya. “I am lets get on please.” Da k’yar ya iya miyar da hankalinsa kan meeting d’in Allah-Allah yake a tashi yaje yasamu flower’nsa se duban rolex agogon hannunsa yake. 4:00PM na bugawa ya hau hanya. Koda k’ofarsu yayi welcoming nasa Fannah bata jiyo ba dake tana chan a d’akinta. Duba kitchen yayi a farko ganin bata chan ya duba d’akinsa nan ma be ganta ba dan haka ya nufa d’akinta a bud’e yasamu k’ofar yana sa kai ya hangota tsaye kan stool tana k’ok’arin miyar da labule da alama ya fita mata ne. A hankali ya tako har zuwa wajen ba tare da yayi making any noticeable sound ba. Har a yanzu bata ji shigowarsa ba. “Flower” ya kira sunan ta cikin wani irin muryan dake sosa mata zuciya. A d’an firgice ta juyo “heyy Anas welcome home yaushe kadawo?” “Just now” ya nuna mata jakar laptop nasa. “Me kikeyi haka?” “D’aya daga cikin masu aikin ne labulen nan yafita mata tun d’azu nake k’ok’arin miyar wa na kas-” bata k’are maganar ba k’afanta ya gauce daga kan kujeran k’ara sosai ta saki cike da tsoro “arghhhhh!!!” Jira kawai take tajita a k’asa danko harta rufe ido chak! taji an cafko ta. Nishi take da zafi zafi, a hankali ta bud’e idanunta ta sauk’esu kan kyakkyawar fuskar Anas. Hannunsa d’aya ya zagaye a bayanta d’aya kuma ya rik’e hannunta da nasa. “Huh!” Ta sauk’e ajiyar zuciya. “Thank you I thought I’d fall.” “Not when I’m around Flower.” Ya sakar mata da brightest smile nasa me k’ara masa kyau. Murmushin ta miyar masa tana k’ok’afin tashi. “Uh-uh” ya kad’a mata kai. Kafin tayi magana ya matso da fuskarsa gab da nata ta yadda suna feeling air da suke breathing. Kallon cikin ido suke ma juna na a k’alla minti biyar sannan daga bisani Fannah tayi gyaran murya sewani bugawa zuciyarta yake “Anas lets go and eat” duk yasata feeling unconfortable. Ignoring nata yayi danko baijin yunwa ta had’a masa lunch yau. Sumbatan goshinta yayi, idanunta ta matse gam take numfashinta ya soya. Murmushi ya saki tare da sake sumbatan idanta na dama haka yayi ana hagu ma, daga chan ya mata a kumatunta duka se tsinin hancinta da hab’anta. Wani irin nishi Fannah ke sam ta kasa bud’e idanunta, ji tayi k’arfin jikinta na raguwa da abinda Anas ke mata. Kansa ya sauk’ar daidai wuyanta yana shunshuna daddad’an turarenta me birkita masa lisafi sannan cikin wani erin salo ya soma raining kisses all over wuyanta. “Anas...” tayi moaning sunansa. “Uhmmm” yayi moaning back har a yanzu be bar showering kisses a wuyanta ba. “Please stop” ta fad’a tana k’ok’arin turesa sede ta kasa, jikinta na marhaba da abinda yake mata sede zuciyarta ce bataso saboda tsoro. Ba k’arya she is enjoying abinda yake mata amman kuma tana tsoro at thesame time. So take ta dakatar dashi tun beyi nisa ba in bahaka ba kuwa asirinta ze iya tonuwa. “Why?” Ya tambayeta a lokacin daya d’ago fuskarsa yadawo dashi kan nata. “Lets go and eat kaji? I’m hungry.” Wani peck d’in yakuma manna mata a kumatu. “Anas kaji? D’agani please.” Wani erin kallon da be tab’a mata irinsa ba yasoma mata ayau, sosai ya razanar da ita, ganin yadda idanunsa suka soya launi lokaci guda gawani erin nishin da yakeyi. I have to stop him, what do I do? Ta tambayi kanta duk ta kid’ime. Fuskar sa yasake matso dashi gab da nata ta yadda tip na hancinsu ya had’e tsoro sosai Fannah keji abu kad’an ya rage bata soma kuka ba. Cikin k’wayoyin idanunta yake kallo a yayinda bugun zuciyarta ya k’aru. Lips nata ya soma laluba abu d’aya ya fad’o mata a rai a wannan lokaci take ta manne bakinta ciki tare da matse idanunta gagam ganin haka yad’anyi baya kad’an. Jin nishinshinsa ya ragu akanta ta bud’e idanun nata kallo d’aya tama Anas taga disappointment karara a fuskarsa ba shakka abinda Fannah tayi ya mugun basa mamaki mesa zatayi shutting nasa? Mesa barata bari yayi kissing nata ba? Mik’ar da ita yayi ta tsaya kan k’afafunta. Cikin cracky voice tace, “Anas I’m sorry” kai kawai ya girgiza mata. Kafin ya juya yace ze fice ta rik’o hannunsa da sauri “Anas please I’m sorry don’t be mad kaji? I’m sorry.” Hannunsa ya fisga daga nata “no Fannah so this is the reason, is that it?” “What reason?” ta tambaya cike da tashin hankali ganin yadda zuciyarsa ke tafasa. “The reason why you haven’t told me how you care about me ashe saboda kinada wanda kikeso ne right? Shiyasa baraki iya barina inyi kissing naki ba is that it?” “Ya Salam! Anas wani erin magana kake? Kaima kasan thats not true.” “Well thats how its looks like, sakemin hannu.” Ya fad’a ba wasa. K’in sake masa hannun tayi “Anas please calm down let me explain kaji? I can’t stand you being mad please.” Hannunsa ya fisge da k’arfi. “What am I to you huh?! Some kind of trash? You can’t even let me kiss you?” Ya fad’a a tsawace kakkarwa tasoma, hawaye na cikowa a idanunta. “Da fili kika fito kika cemin kinada wanda kikeso you wouldn’t have hurt me like this Fannah, I’ll understand you but with what you did...” Kasa k’arisa maganan ma yayi dan yadda abinda ta masa ke ci masa rai, he is so disappointed ai inhar kanason mutum baraka damu ba dan yayi kissing naka, in bawai Fannah nada wanda takesoba ba yadda za’ayi tayi shunning kiss nasa haka, sekace wani trash. Kai kawai take kad’a masa hawaye tsilli-tsilli na sauk’a akan kumatun ta tana k’ok’arin lalimo hannunsa “no don’t touch me, don’t f*cking do that okay? don’t you ever do that.” ya kashe mata warning dataji har abada batason sake rik’e masa hannu dan yadda ta tsorata. “In few months time conctract d’in ze k’are you are free sekije ki samu shi wanda kikeson, its what you want anyway.” ya watsa mata wani erin pathetic kallo, yana kaiwa nan ya fice. Kuka ta soma “no Anas please don’t go kaima kasan banida wanin da nakeso please kayi hak’uri...” haka tata binsa har k’ofar d’akinsa tana had’asa da Allah tana basa hak’uri amman ko sauraronta beyi ba seda yakai k’ofar d’akinsa kafin ya rufe ta sa hannu ta taresa. “Anas please kar ka min haka I have a reason for shunning your kiss-” katseta yayi; “Sure yes you do Fannah and I understand saboda kinada wanda kikeso koba haka ba? Kina ajiye mishi kanki kin kyauta sosai.” Hannunta yacire daga jikin k’ofar ya buga bam! A fuskarta. “Anas pleeaaassseeeeee!” ta fashe da kuka... *© miemiebee* beeenovels.blogspot.co.ke [12:57, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 6⃣7⃣ Buga k’ofar take tana hawaye. “Anas please open up kaji? Kayi hak’uri dan Allah... I’m sorry Anas pleaseee...” Yana mik’e akan gado ya zura wa ceiling ido, idanun nasa sunyi ja zir yana sauraron duk k’aran da takeyi amman baijin ze iya bud’e mata ya saurareta. Why does love hurts? Tunda yake Fannah ce macen daya fara so mesa zata masa haka? Was he too quick? Even still be kamata tayi shunning nasa haka ba it was just a kiss bawani abu nayi niyyan mata ba was she too afraid? Oh no! “Anas please ka bud’en kaji? Yi hak’uri dan Allah” Tagaji da tsayawan ta koma zama, k’arfin jikinta har ya k’are buga k’ofan ma takasa yanzu se hawaye kawai take. Da k’yar ta tattara kanta ta koma d’aki layin Anas ta kira yana gani har call d’in ya yanke yak’i picking ta dad’a masa 5 missed calls akai ganin he is not ready ya d’aga tayi texting nasa _Anas please pick up your phone koda baraka bud’e k’ofar ba pick up the call kaji? I’m sorry we need to talk._ “We have nothing to talk about Fannah” ya fad’i a fili tare da miyar da wayar nasan ya ajiye a gefe. Sake trying layin nasa tayi yana ji yana gani nan ma yak’i d’agawa. Bayan kamar minti talatin daidai 5:30PM ta dawo k’ofar d’akin san. “Anas bakaci abinci ba ka fito kachi kaji? Karka zauna da yunwa please yi hak’uri.” K’ofar ta buga “Anas? Anas nasan kanaji na please ka bud’e” nan ma haka tata suratan duniyan ta befito ya bud’e ba. _7:40PM_ A hankali ya bud’e k’ofar d’akinsa ya fito sanye yake da ¾ wando ash da farin vest. Yunwa ne ya fitine sa, tafiya yake yana addu’a Allah sa kar ya had’u da Fannah. Zaune a parlour yaganta ta had’a tagumi ko noticing nasa batai ba seda ya k’are mata kallo nakusan minti biyu sannan ya nufa dining area ya bud’o fridge anan ne tagansa. “Anas!” ta kira sunan sa ganinsa kad’ai taji damuwanta sun d’an ragu barata iya jure shirun Anas ba, baro inda take tayi ta nufa wajensa. Roasted chicken yaciro danko bai tunanin ze iya chin abincinta. Ganin haka tace, “Anas yanzu baraka chi girkin dana maka ba?” ta tambayesa idanunta na cikowa da hawaye. “Kayi hak’uri dan Allah, please ka zauna kaci abincin kaji? Wannan kazan ba rik’e ka zeyi ba.” so take ta rungumosa amman tana jin tsoro tasan Anas da banzan zuciya inba wani ikon Allah ba bare sake mata magana ba yanzu, babban tsoron ta kenan. Wata zuciyar ce tace mata to ki fad’a masa gaskia mana he will understand you, kai ta girgiza. Ko saurarenta beyi ba yaciro coke ya fice binsa take tana roqonsa har suka shiga d’akinsa amman ko sauraranta baiyi. “Anas wai baraka min magana ba? I said I’m sorry bawai nayi hakan bane saboda inada wanda nakeso, Anas I have no one apart from you, you know that koba haka ba? Dan Allah Anas talk to me” ga hannunsa nan tana son ta rik’e amman tsoro bare barta ba da zaran ta tuna irin warning daya kashe mata d’azu haka tana ganinsa yagama cin kazan sa ya kora da drink ya miyar da plate d’in kitchen. Bayan dawowansa ya zauna kan gado tare da juya mata baya, laptop nasa ya ciro ya soma soma aiki akai. “Anas I get it you are mad at me amman kayi hak’uri ka tashi muyi Sallah kaji?” Dadduma ta shimfid’a musu. “Anas lets pray ka tashi.” Bema san tanayi ba duk suratan da takeyin nan besan tanayi ba hankalinsa ya tattara ya miyar kan laptop nasa. Zama tayi daga bakin gadon chan ta d’an tattara kayansa daya cire d’azu tasa a laundry basket dawowanta ta jeta ta tsaya akansa. “Anas wai baraka min magana ba? Anas I’m talking to you” ganin baida niyyan koda kallonta ne tasa hannu ta rufe laptop d’in ita kanta bata yi tunanin zata iya hakan ba. Anan ne ya d’ago kai ya aza blue eyes nasa akanta. “Anas I said I’m sorry lets talk please wannan sharenin da kakeyi ba abinda ze haifar mana please kaji lets talk.” Kamar wanda bareyi magana ba chan ya nisanta yace, “we don’t have anything to talk about sabida banida abinda zan ce miki.” Yana kaiwa nan ya d’au laptop da wayoyinsa yabar mata d’akin. “Anas dan Allah karka sake tafiya...” ta sauk’a har k’asa tana kuka tafi minti ishirin zaune a k’asa sannan ta tattara duka k’arfinta ta tashi if only zata iya fad’a masa da tayi amman batta tunanin zata iya, tsoro kad’ai bare barta ba gani take kamar inta sanar dashi LABARIN TA (littafin pherty) ze guje ta abinda barata iya jurewa ba kenan. Parlour ta lek’a tagansa yana Sallah hawayen dake k’ok’arin fito mata ta matse sannan ta koma d’akin itama ta idar da nata. Kayan baccinta tasa ta haye gadon ta kwanta badan tana jin bacci ba dan de batasan nayi ba tunanin Anas nata kawai take. Jiran shigowar sa take tun d’azu amman shiru har kusan 11:40PM Anas be shigo ba koda ta leqa parlour taga bayya chan. D’akinta ta duba chan ma bata gansa ba sauran d’akunan ta bi one by one kap bata ga Anas ba hankalinta in yayi dubu be tashi ba guest room taduba a k’arshe a hankali ta bud’e k’ofar ta tsince sa kwance kan gado yana bacci wani sabon kukan taji na k’ok’arin fito mata. Bayan ta shiga ta miyar da k’ofar ta rufe kan gadon ta k’arisa ta kwanta agefensa bayan ta had’a musu pillow. Hannunsa ta d’aga ta had’a da nata sannan tasa a k’ark’ashin kumatunta data kwanta akai. Kallonsa take ayayinda idanunta ke cikowa da hawaye “Anas I’m sorry if only I can tell you da nayi I love you so much” matso da fuskarta tayi tare da pecking nasa a kumatu sannan ta koma ta kwanta ahaka har tasamu tayi bacci ko data soma mafarke-mafarkenta sake matsowa tayi kusa da Anas ta dandame hannunta da nasa. Asuban fari Anas ya tashi sosai yasha mamaki ganin Fannah kwance a jikinsa a hankali ya raba jikinta da nasa, hannunsa data matse cikin nata tak’i sakewa yayi qoqarin rabawa amman ya kasa daga k’arshe tapping nata yayi seda ta tashi daga baccin. Da sauri ta sake masa hannu “I’m sorry” ta fad’i bece mata komai ba ya mik’e yabar d’akin zuwa nasa achan yayi alwala yayi Sallah yasa alarm nasa da ze tada shi dan shirin office. _7:10AM_ Cike dining table nasu ke da abinci daban daban iri-iri bata tab’a shirya masa breakfast me yawa kamar na yau ba. Lab’e take a kitchen tana jiran fitowar Anas 7:23AM ya fito yayi shiri all in black meaning he is in a bad mood today, yau akwai firing mutane a office kenan. Binsa da kallo take, hararan foodwarmers na kan table d’in yayi sannan ya nufa fridge yaciro ragowar kazan sa na jiya nan tafito daga wajen b’uyan nata. “Anas good morning” ta gaishesa ko kallonta beyi ba. Coffee data had’a masa ta tsiyaye a cup. “Anas take your coffee” nan ma banza da ita yayi chin kazansa yake a hankali ganin batada niyan daina damunsa ya mik’e a fusace batasan lokacin data rik’o hannunsa ba. Wani irin wawan kallo ya watsa mata da kanta ta miyar da hannun nata baya. “Anas I’m sorry atleast kabani chance inyi explaining kaina please.” Bece da ita komai ba ya d’au jakar laptop nasa ya kama hanyan fita binsa tayi da lunch data had’a masa ba rok’an duniyan da bata masa ba ya amshi lunch d’in amman yak’i har parking lot ta rakasa amman ya bonsa ta yayi tafiyarsa. Ciki ta dawo tana kuka batasan me zata ma Anas ya saurareta ba. Rabinta nace mata ta tsaida sa ta fad’a masa reason dayasa tayi shunning nasa kamar yadda sauran rabin nata ke ce mata karta fad’a masa. Kwata-kwata batasan nayi ba wanka ma dak’yar tayi wedding photos nasu ta d’au tana sake kallo daidai kan wanda take kallonsa har yake mata dariya lokacin, ta tsaya ta d’au hoton a wayarta ta masa sending a whatsapp tare da adding caption _Anas I will always look up at you. I’m sorry please come back home and I’ll explain everything banida kowa banda kai please and kar kayi firing workers naka saboda laifin danayi please... Kaji?_ Alokacin daya gama sanar da Kacallah yaje yayi firing mutane biyar kenan sak’on Fannah ya shigo bayan ya karanta seyaji jikinsa yayi sanyi, Kacallah ya kira a waya yace yadawo wa mutanen da aikinsu. Fried rice me rai da lafiya Fannah ta girka musu yasha kayan had’i sosai, bayan tagama ta jera dining table sannan ta sake wanka taci kwalya sosai. Wata shegiyar english gown taciro daga cikin akwatin english wears nata. Kaya ne had’ad’d’en k’arshe gown ne har k’asa amman an tsaga shi daga k’asa zuwa har wajen guiwa ta gefe. Hannu d’aya garesa shima spaghetti hand ne seta sa seta sake cirewa kunya bare barta ta bari ba. Haka ta tayi ganin lokaci na k’urewa ta dage tasa bata sake cirewan ba, kallon kanta tayi a mirror yadda kayan ya tafi da surar jikinta ita kanta tasan tayi kyau amman kayan yayi tsireci mata da yawa bata tsammanin zata iya fitowa gaban Anas ahaka. Gashinta tayi oiling ta taje da k’yar seda ta kusan hawaye sannan tasamu ta kama gu d’aya kamar ranan ta zaro kad’an a gaba ta kitsasu sosai tayi bala’in kyau sede duk wannan uban kwalya ta d’aura hijabi akai. Ganin k’arfe hud’u ya buga in less than 20minutes Anas ze k’ariso taji bugun zuciyarta ya tsananta tayi niyyan a yau zata bayyana masa sirrin dake zuciyarta itama ta fad’a masa tana sonsa takuma sanar dashi dalilin dayasa tayi shunning kiss nasa jiya. Ido ta rufe a sannu a sannu tacire hijabin ta koma gaban mirror ta k’are wa kanta kallo, d’an k’irjinta daya fito daga kayan ta dannesa ciki, tana dannewa yana sake fitowa data gaji tabari. Parlour ta koma ta zauna kan kujera se fad’i gabanta yake a yayinda take ta matse tsagun dake jikin kayan. 4:23PM Anas ya dawo gida k’ofar na bud’uwa Fannah ta bayyana a bayansa. Baki ya sake tare da zaro blue eyes nasa in shock yana kallonta, wace wannan kyakkyawar halittan dayake gani a gabansa? Kallonta yake daga k’asa har sama yayi haka kusan sau uku still yakasa yarda Fannah ce everything about her is perfect seji yake kamar yau ya soma sata a ido bebar kallonta ba har yanzu ga wani murmushin dake d’auke fal a fuskarta wanda ya k’ara mata kyau ji yake kamar ya had’iye ta dan kyau. Shin mesa bata sa masa irin kayakin nan kullum, dama haka Fannah take da innermost kyau? Masha Allah gaskia yayi sa’ar mata, matar da bata sonsa matar da take son wani na daban ba shiba. Wannan tunani na tab’o sa yayi k’arfin hali ya kawar da kallonsa daga gareta da k’yar. K’ofar ya miyar ya rufe seda yazo wucewa ta gefenta tasa hannu ta dawo dashi baya da k’arfin da Allah ya bata. Jakarsa ta amshe kafin yayi magana tace, “welcome home mijina.” Kallonta ya tsaya yi danko bata ishesa da kallo ba idanunsa da suke kai kansu kan k’irjinta yake ta k’ok’arin miyar dasu kan fuskarta. “Anas we need to talk ko seka chi abinci?” “Bani jaka na” yace da ita. “No Anas I will not let you go this time around you must listen to me Anas, nagaji da wannan sharenin da kakeyi I can’t take it anymore, kad’au dan inaso ne nayi shunning naka iyyeh? Kuma kamar ya zakace ina da wani wanda nakeso sanin kanka ne banida kowa sekai.” Tad’anyi shiru hakan yabawa Anas daman magana “kin gama? If yes bani jaka na in wuce.” “Anas wai dan Allah baraka bari ba? Look at me! Look at me Anas!” Ta fad’a a tsawace for the first time “I dressed in this alluring (attractive) manner just to impress you inda dagaske inada wanin da nakeso ai barin bari kaga jiki na haka ba.” “I should have guess, excuse me” ya watsa mata kallo sannan yabi ta gefenta hannunsa ta kama ta dawo dashi baya. “Fannah bance miki karki sake tab’ani ba? Ban-” katse sa tayi; “I don’t care! I don’t bloody care Anas” ta fad’a a tsawace. “You are my husband addini na be haramta min tab’a ka ba.” Hannun nasa ta sake kamawa “Anas na tab’aka na rik’e maka hannu so what? Why are you giving me such a hard time? Can’t you also see? Anas I love you. I love you Anas Ibrahim Fauzi and tab’aka yau na soma haka kawai baraka sa min hauka ba tun jiya nake binka kak’i min magana kona maka girki baka ci for what? Saboda nayi shutting naka? Ban barka kayi kissing d’ina ba? Is that it? Well here I am kiss me Anas if it will ease your anger kiss me. Haba mana! I love you Anas shirunka agareni babban tashin hankali ne. Yanzu wuce muje kachi abinci mucigaba daga inda muka tsaya.” Ta k’arasa maganan a tsawace tana masa nuni da daining area. Ita kanta batasan ta iya masifa haka ba inma ta iya bata tab’a tsammanin zata iyayiwa Anas masifa ba har ya tsaya yana sauraronta be zubar mata da hak’waranta a k’asa ba. Mamaki ne sosai yacika Anas anya kuwa wannan ce Fannar daya sani wanda ko magana bata iyayi da k’arfi shine take wannan uban masifan daya d’an basa tsoro shi kansa? Hannunsa taja ta katse masa tunani. Kujera taja mishi tare da zaunar dashi nan tayi serving nasa abincin. “Eat” ta fad’a masa. Ba musu bale gardama ya soma chi juice ta tsiyaye masa haka tana tsaye akansa har ya gama chi. “Zaka k’ara?” ta tambaye sa Kai ya kad’a mata kamar d’an yaro. Yana gamawa ya mik’e gabansa tasha. “We are not done yet Anas.” se a yanzu bakin sa ya bud’u. “Yes we are” ya fad’a a tsawace. A tsawacen itama ta mayar masa “no we are not because I love you Anas dan Allah ka dena wahalar dani haka I’m sorry for what I did to you yestarday. I’m so sorry please.” “No you are not Fannah.” “Anas I am wallahi I am, I love you.” “Then prove it Fannah inhar dagaske kike you love me prove it to me.” Taku d’aya tayi tare da rufe gab dake tsakaninsu. Hannayenta biyu ta aza a side na fuskansa. “I love you and I will prove it.” D’agel d’in kafa tayi ta d’an kamo sa a tsayi. Ya bud’e baki zeyi magana kenan tayi shutting nasa dawani hot kiss. Mutuwan tsaye Anas yayi sosai Fannah ta basa mamaki yama kasa d’aukan abinda ke faruwa a k’wak’walwarsa be tab’a kawo wa a ransa Fannah zata iya kissing nasa ba, ita da kanta bata tab’a sanin zata iya aikata abinda ta aikata yanzu ba all she know is that she wants to prove to him she loves him. A hankali ya d’aga hannayensa ya zagayesu a ‘yar k’wank’wasonta tare da sake pulling nata closer to him. Hannunta ta d’aga itama daga fuskarsa ta miyar cikin gashin kansa me uban yawa sun d’au tsawon lokaci suna abu d’aya sannan a hankali tayi pulling out nishi suke dukansu da k’arfi. Ba wanda ya iya yace ko uffan cikinsu they are both still shocked. Kanta ta sunkuyar har yanzu ta kasa believing abinda tayi sede kuma she enjoyed kissing Anas it was worth it. Kallonta yake na kusan minti d’aya ganin batada niyan d’ago kai ko cewa wani abu yasa hannu k’ark’ashin hab’anta ya d’ago fuskarta har ayanzu tak’i barin su had’a ido lips nasa ya lasa yana wani irin shegen murmushi. “Flower...” Ya kira sunan ta cikin wani irin salon dake sosa mata zuciya. *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:57, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 6⃣8⃣ Kasa koda amsashi tayi wani kunya taji ya rufeta, she can’t believe abinda ta aikata sede kuma chan cikin zuciyarta tana miradi da abinda tayi atleast tayi proving masa tana sonsa bare sake kokwanton san da take masa ba. Hannunsa ta sauk’e daga hab’arta tare da juyawa kafin ta soma tafiya yasa hannu a kunkuminta ya juyo da ita tare da matse jikinta a nasa. “Flower look at me” har a yanzu tak’i d’ago kai su had’a ido. “Flower baraki kalleni ba?” Kai ta kad’a masa. “Then look at me” kai ta sake kad’a masa kunya bare barta ta kallesa ba. “You love me right?” Ya tambayeta. Kai ta gyad’a masa. “I want to hear it again Flower.” Hannunta ta zagaye a bayansa tayi hugging nasa “I love you Anas, I love you so very much *My Lion”* shima a hankali ya zagaye hannayensa a bayanta pulling her closer to him. Gashinta yayi kissing “I love you so much more Flower.” sosai yaji dad’in sunan data kirasa dashi *•°LION°•* it means everything to him. Sun d’au tsawon lokaci suna atsaye sannan a hankali ya raba jikinsa da nata tare da jawo hannunta suka zauna kan kujera. Hannyensu ya had’a duka waje d’aya cikin sanyin murya a hankali yace, “Flower fad’amin mesa kikayi shunning d’ina jiya? Nasan kina da qwararren dalili koh?” Kai ta gyad’a “then tell me kinji? Karki b’oye min tell your husband” Innocent eyes nata data k’ayatasu da kajol ta d’ago a hankali ta azasu akansa. “I’m afraid Anas tsoro nakeji” ta sanar dashi cikin cracky voice. “Tsoron meh Flower? Kin d’au zan miki wani abu neh?” nan ma kai ta gyad’a. “Don’t be kinji? Ba abinda zan miki seda yardan ki I will never do anything to you ki saki jikinki dani kinji?” Batasan lokacinda hawaye yasoma ciko mata a ido ba cikin sautin kuka tace, “for how long Anas? For how zaka ta zama haka? For how long zanta toye maka hak’k’in ka?” “For as how long it takes Fannah ni ban damu ba I love you so kema kibar damuwa kinji?” Kai ta kad’a “Anas dole in damu saboda na miji ne kai dole wataran sha’awah ze taso maka and saboda bakason kayi forcing d’ina seka hak’ura ka tauye wa kanka hak’k’i saboda matarka batason baka hak’k’inka? In hakan ya faru kasan me mala’ikum Rahma zasu min? Anas tsine min zasuyi, zasu tsine min...” ta fashe da wani irin matsanancin kuka. Duk tabi tasa Anas rikicewa a rayuwa ba abinda ke tada masa hankali kamar kukan flowersa. Matso ta yayi ajikinsa yana bubbuga bayanta “Flower kibar kukan nan please I can’t take it please kibari kidena.” Pecking gashinta yayi “stop crying kinji? Ba tsinuwan da za’a miki in shaa Allah ni nayi deciding I won’t touch you se in rananda kika yarda so kibar kukan kinji?” Kai ta gyad’a masa a hankali tasoma shanye kukan nata. Seda ya tabbata tayi shiru ya d’ago ta daga jikinsa yana kallonta “Flower but what are you so afraid of? Mesa kike tsoro haka? Saboda kin ganni kind of large?” Ya tambaya tare da d’age gira. Murmushi kad’an ta saki tana kad’a kai danko yabata dariya shi ya d’au wai tsoronsa take amman ko kad’an. “Tsoro na kikeji flower?” Kai ta girgiza masa “mesa zanji tsoron ka *Cherie Pie?”* “I don’t know kodan kinga inada builded body kinga muscles all over my hand kike tsoro I might destroy you on bed kekuma gaki ‘yar k’arama” Dariya sosai ta tsaya tanayi harda rik’e cikinta. “Anas I’m not small kadena cemin small.” “Yes you are Baby and thats why kike tsoro.” “Ko kad’an ba haka bane *Doodle bug* matsalar ba daga gareka bane...” Sekuma tayi shiru take mood nata ya canza. Hannunta ya rik’o “ba daga ni ba Flower? Bani kike tsoro ba?” Kai ta gyad’a masa “toh daga waye ne Flower?” Take idanunta suka ciko da hawaye “Anas daga ni ne, matsalar daga ni ne...” Sekuma ta fashe da kuka. Hankalin Anas in yayi dubu be tashi ba kamar ya daga ita? Me take nufi? Mesa take kuka haka? Is she lacking something as a woman? Subhanallah! Kwanto da ita yayi a kan k’irjinsa yana fad’a mata dad’ad’d’un kalamu masu kwantar da hankali. Duk yabi ya k’osa yaji dalilin dayasa take tsoron had’a kwanciya dashi. Seda ya tabbata tayi shiru ya d’ago ta tare da rik’o fuskarta da hannayensa bibbiyu. “You don’t have to be afraid anymore, Flower ko a yaya kike I love you koda you are lacking something as a woman I still love you ahakan ina sonki nake tsakani da Allah badan wani abinda kike dashi ba.” Idanunta taji suna sake cikowa da hawaye “Anas koda... Koda...” sekuma ta sake fashewa da kuka. Haka ya sake rungumota seda tayi kukan me isarta sannan ta taso da kanta, hannunsa ta rik’e cikin nata tana kallon cikin idanunsa da kumburarrun idanunta da sukayi ja “Anas I’m insecure of your love gani nake kamar I’ll lose you, gani nake kamar in na fad’a maka sirrina zaka gujeni ka nisanta daga gareni ka kuma tsane ni, abinda baran iya jurewa ba kenan, I don’t want to lose you My Lion.” “Flower I will never hate you kibar fad’an haka, I will never leave your side koda kuwa wannan sirrin kin is as worse as kisan kai God forbid I will never leave you Fannah. I love you for the sake of Allah and nothing more ki d’au wannan sirrinkin k’addara ne a rayuwar aurenmu kinji? And stop saying zakiyi losing d’ina kinji na rantse I will never leave you, never.” D’an sanyi taji a ranta duk da cewa kuwa bata gamsu ba acewarta Anas na fad’in hakan ne dan besan ba cikakkiyar budurwa ce ita ba. “So can you tell me? Zaki iya fad’amin dalilin dayasa kike tsoron wani abu ya shiga tsakani na dake? trust me koda mene barin tab’a barinki ba Flower *_INA TARE DA KE”_* kai ta gyad’a masa tsili-tsilin hawaye na gangarowa kan kumatunta wanda yasa hannu ya share. “Anas kayi hak’uri dan Allah kasani bawai nayi hakan bane dan cin amanarka, I just can’t bring myself to tell you I’m.. I’m not complete as your woman I’m lacking something. Anas banida... Banida...” sekuma kuka yafi k’arfinta. Zuciyarsa yaji ya buga tsoro shi kansa ya somaji. “Shhhh is okay” yayi hugging nata “ya isa you can’t talk right now ya isa kinji? Mubar maganan” sosai hankalinsa ya tashi shima yarasa meke masa dad’i me Fannarsa ta rasa? Mesa da zaran ta tuna abin take kuka? Ko kad’an be kawo a ransa wai ko nufi take batada budurci ba saboda yasan hankalinta ya yaba da tarbiyyan ta yasani barata tab’a siyar da budurcinta ma kowani k’ato ba. Seda ya tabbata tayi shiru yace da ita “tashi muje d’aki ki kwanta kinji?” “Anas I’m sorry trust me I really want to tell you, wallahi inason sanar dakai I can’t-” katse ta yayi “I trust you My Flower shikenan don’t bother kinji? Mubar maganan I trust you ko baki fad’a min yau ba you will some other day ko ba haka ba?” Kai ta gyad’a. “Shikenan tashi muje d’aki.” Tana manne ajikinsa suka k’arisa d’aki ya kwantar da ita ajikinsa har a yanzu nishinta be dawo normal ba yana bubbuga bayanta har tasamu tayi bacci. “Flower” yakira sunanta. Jin shiru yad’an lek’a fuskarta yaga tayi bacci. Hannunsu ya had’a “Fannah I love you kinji? Banga abinda zesa in barki ba no matter what _*INA TARE DA KE_* forever” ahaka shima yasamu ya kwanta da tunanin Fannah a ransa. ***** Seda Maghrib Fannah ta tashi a hankali ta raba jikinta da nasa ta fad’a toilet bayan tagama duk abinda zatayi tafito tayi kan Anas cikin wani irin romantic salo ta tayar dashi daga bacci yayi alwala shima yajasu Sallah. Bayan sun idar suka ci dinner, kallo kad’an suka tab’a suna hira suna tambayan junansu questions about likes and dislikes nasu dakuma age da sauran abubuwa da dama. Sosai shekarun Anas ya bata mamaki ashede mijin nata yaro ne ko 25 be cika ba gashi kuma ajebo abubuwa dayawa bayya chi. Haka suka tayi har zuwa 10:00PM sannan suka koma d’aki shi da kansa yaciro mata rigar baccin dayakeso tasa. “Babe wannan?” ta tambaya tana zaro idanu waje “Ai wannan ba marabansa da babu jibi fah.” ta d’aga shimen sama. “Flower shi nakeso.” Wani daban taciro “zansa wannan.” “A’a flowor ni wancan nakeso” zata sake magana yace, “zanyi fushi in baki sa ba” da sauri ta katse sa, “a’a karkayi zansa.” murmushi ya saki yana binta da kallo ta shige d’akinta ta koma tasa tare da k’are wa kanta kallo jikin mirror. Kai ta kad’a no gaskia yayi tsireci dayawa wata zuciyar ce tace mata toh ai mijin ki ne bawani gardi ba. Sam ta kasa fita da kayan hijabi ta b’urma akai tana kai k’ofan d’akinsa ta tsaya daga bakin k’ofar a nitse ta bud’e k’ofan kad’an nan ya maido da kallonsa wajen. “Come in Baby” ya buk’ace ta. Ido ta rufe ta cire hijabin da k’yar ta iya shiga cikin d’akin kanta a k’asa se murza hannayenta take duk kunya yabi ya cinyeta kallonta ya tsaya yi wane yau ya soma sata a ido ji yake kamar ya had’iyeta ko kyafta ido ya kasa why is she so damn beautiful? Abinda yake ta nanatawa a ransa kenan. Da kallon ya isheta seta fara k’ok’arin miyar da hijabin nata kamar a kyaftawan ido ya k’ariso gabanta tare da k’wace hijabin. “Anas kabani please.” Murmushi ya saki me k’ara masa kyau. “Flower you are damn beautiful” hannu yasa ya zagaye a kunkuminta ya matso da ita kusa dashi. “Kiss me” ya buk’ace ta. Yi tayi kamar bata jisa ba. “Flower I said kiss me.” Kai ta d’ago ta k’are masa kallo sannan tayi d’agel ta yi pecking nasa a kumatu. “There bani hijabi na toh.” “Are you kidding me? Kiss me like you did d’azu.” “Barin iya ba” ta fad’a stubbornly. “Nima barin bada hijabin ba.” “Anas please kabani.” “Kiss me first.” “Okay naji sakeni toh.” Kafad’a ya buga mata. “Ka sakeni toh I will kiss you.” “Are you sure?” “Yes My Lion.” Ba musu ya saketa hannunta ta zagaye a wuyansa sannan ta k’are wa light red lips nasa kallo seda ta tabbata ya shagalta yana jiran tayi kissing nasa tasa hannu ta fisge hijabin ta ta haye kan gado a 360 tana mai dariya. Murmushi ya saki ya juyo yana kallonta se faman dariya take masa. “Kin min wayo koh?” Abinda yace da ita kenan. Dawowa yayi ya haye gadon shima tare da k’wace hijabin hannun nata jawota yayi ya haye kanta se faman chakulkuli yake mata itako se dariya take harda hawaye tana basa hak’uri ya dena sam yak’i chan zuwa shad’aya suka kwanta a gajiye dan wasan da suka tayi sukayi bacci. _7:42AM_ Yanzu su Fannah suke gama breakfast. Yau breakfast d’inma a plate d’aya suka yi har suka gama tana zaune a kan cinyarsa, tabashi ya bata ahaka har suka gama karyawan. Tayasa tayi ya gama shiri sannan ta rakosa har bakin k’ofa ta miqa masa lunch pack nasa. “My Handsome” ta kirasa. “Yes Flower.” murmushi ta saki masa; “Yau in ka dawo I’ll reveal my secret for you. Kai mijina ne be kamata ace ina b’oye maka wani sirri na ba zan fad’a maka komai” “Are you sure Babe?” ya tambayeta. “Yes I am, na yarda da kai dakace baraka barni ba koda kaji wannan sirrin nawa so zan fad’a maka My Husband Baby.” Taku d’aya ya k’ara ya rufe gab dake tsakaninsu. “I will never leave you Flower I love you” yayi pecking nata a goshi. “I love you too My Lion take care of yourself for me kaji?” “I will Baby.” “Me kakeso in dafa maka yau?” Ta tambayesa tana gyara masa necktie nasa daya d’an gauce. “Anything yummy” ya kashe mata ido. “Okay toh I will cook your favorite” “Kina nufin pounded yam da Eghusi soup?” “Yes Baby off you go I love you.” Kai ya girgiza mata cike da rashin fahimta ta tambayesa “why?” “You don’t love me” yace da ita. “Ofcourse I do My King I love you kadena fad’in haka zuciya na bare iya d’aukawa ba.” Hannu yasa ya taro fuskarta. “Flower bakiya sona, in har kina sona be kamata ace zan fita office baraki bani ko d’an goodluck kiss ba.” Murmushi kad’an ta saki “dalilin dayasa kace bana sonka kenan Baby?” Kai ya gyad’a. ‘Yar murmushi ta saki “wannan bare kawo fad’a ba My Lion.” D’agel d’in k’afa tayi tare da zagaye hannayenta biyu a wuyansa sannan tayi kissing nasa passionately ba kamar jiya da tanayi zuciyarta na bugawa ba, kissing nasa take fiye da yadda tayi jiya duk sun zurfafa cikin abinda sukeyi daga bisani tayi pulling out. Kallon idanun juna suke suna murmushi peck ta manna masa a duka kumatunsa one-by-one sannan tip na hancinsa tayi tayi ta masa a goshi amman takasa dukda d’agel d’in k’afa da tayi. Daya gano haka seya sa hannu ya d’aga ta sama nan ta manna masa peck a goshin sannan ya sauk’e ta. “Here are goodluck kisses seka dawo koh? I love you.” Hugging nata yayi “I love you too Flower” daga nan sukayi ba-bye wa juna ya fice. Kan kujera ta fad’a se blushing take tana fad’in “love is the sweetest thing” a ranta “His lips are sweeter than everything and his eyes? OMG!” throw pillow taja ta rufe fuskarta dashi. Shima Anas yana tuk’i amman hankalinsa na akan irin kiss da sukayi sharing da Fannah, “your lips are probably the most sweetest thing I’ve ever tasted Fannah.” _3:25PM_ Fannah tagama duk wani aikin da zatayi, abinci na nan ready ajiye kan dining wanka ta sakeyi tasa wata black lace me torches na pink wanda ya bala’in tafiya da surar jikinta. D’aurin network ta kashe me kyau ta tsara kwalya sannan ta feffeshe jikinta da turare masu k’amshin bala’i. D’akinsa ta shiga ta bud’e wardrobe nasa haka kawai taji bari ta gyara masa dukda kuwa a gyare yake neman abinyi kawai take. Drawer’n under wears nasa ta bud’e ta zazzagosu acikin haka diary nasa data soma karantawa da jimawa ya fad’o. A nitse ta d’aga ta miyar ta soma ninke masa boxers da shorts nasa kap ta gama se fad’a mata zuciyarta ke ta bud’e diary’n ta karanta ai matarsa ce ita abinda zata sanar dashi sirrinta itama yau toh se meh dan ta karanta nasa? Hannu tasa wane ana ganinta ta zaro diary’n kwad’o tagani datse a jiki nan tashiga neman key’n cikin inda yake adana cufflinks nasa tasamu ta bud’e. Flipping first 3 pages d’in tayi saboda ta tab’a karantawa. A page 4 d’in taga heading an rubuta da manyan bak’i THE UNFORGETABLE INCIDENT (THE GIRL) Wani irin kishi taji ya gulleta wani girl yake nufi? Dama Anas nada wata bayan ita? So she is not his first love as yadda ya fad’a mata jiya? Bata hankara ba taji hawaye na cikowa a idanunta (Toh fa Fannah uwar kishi) tsuka taja tare da juya pegin ita a dole kishi barata karanta ba. Kujera tanema ta zauna ta soma karanta rayuwarsa na London tana murmusawa tana jin wani sabon sonsa me d’anko yana sake k’aruwa a birnin zuciyarta da zaran taga wajen daya rubuta yasha barasa sekuma ta had’e fuska. Dogon tsuka taja sanadiyar ganin mafarke-mafarken yarinyar datake da tabbacin itace wanda yake nufi a page 4 na littafin. Wato ma itace yarinyan dayake mafarkinta time to time yana ce min *_TANA TARE DA SHI?_* Koh” “Wallahi Allah kawo ka Anas gaskiya barin yarda ba, waima wace wannan yarinyan?” Duk wannan magana da take a fili take yinsu. Page 4 d’in ta koma ta bud’e tasoma karantawa kamar haka...; *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:57, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 6⃣9⃣ _Saturday evening Bama, Maiduguri Borno._ Dakata karatun tayi mamaki shimfid’e karara a fuskarta “dama Anas yayi zaman Bama? Wow! Tsaya tukuna ko achan na tab’a ganinsa? Yes definately shiyasa rananda muka sake had’uwa dashi anan Maiduguri naji natab’a ganinsa somewhere ashe a Bama ne. Wow!” Murmushi ta saki ta cigaba da karantawa. _It pains me writing this, I can’t forgive myself for what I did to this 15 years old girl. I’m so so sorry, I was drunk I didn’t know what I was doing. I blamed everything on her nayi blaming nata akan laifin da ba ita ta aikata ba I’m so sorry I hope we meet in the future saboda in nemi gafararki. Tun rananda abun ya faru na rasa sukuni a rayuwa, I’ve been living a life of guilt. Kullum cikin mafarkin ta nake I don’t know ko tana raye ko ta mutu saboda sautin kukan ta da suke min yawo akai har a yau. Bansan wani erin k’uncin rayuwa na tusa ta ciki ba, believe me wallahi I had no intention of doing so to your precious life. I was densed, stupid and young lokacin my past kept on hunting me sanadin abinda Ummimi tamin my own MOTHER._ _Da yammacin ranar Asabar, 23rd March 2012_ Dakata karatun tayi “Innalillahi wa inna ilaihi raj’un!” ta furta cike da rashin yarda tana kad’a kai take idanunta suka cike da hawaye rawa jikinta ke sosai yana bata wai itace wannan yarinyan da Anas yake nufi itace wacce *_TAKE TARE DA SHI_* a kullum “Ya Allah karka tabbatar min da abinda nake zato 23rd March shine ranar da aka k’wace min budurcina aka rabani da martabana na k’arfi da yaji.” Hawayenta ne ya d’iga kan page d’in a yayinda tayi k’arfin hali ta cigaba da karantawa. _I wrecked a 15 years old girl, nayi raping ‘yar yarinyar da bansan wace ita ba, bansan ya take ba bansan kotana raye kota mutu ba yanzu. Her words are forever stocked in my head._ _“Dan girman Allah bawan Allah kayi hak’uri I beg of you please. Bawan Allah dan Allah kayi hak’uri I'm just 15 ba abinda zan iya baka have mercy on me please dan Allah.”_ Rufe littafin tayi cike da tashin hankali a yayinda hawaye ke ambaliya a fuskarta kanta yana wani irin juyi ga kuma wani jirin da ta soma ji yana neman d’ibanta tabbas bara tab’a mancewa da wad’annan kalamu ba. Kalamun data ta nanata wa mutumin dayayi raping nata haka tata rok’ansa amman haka ba imani ba tsorom Allah ya danne ta yayi raping nata. Kasa rik’eta k’afafunta sukayi ta sauk’a k’asa se “Innalillahi wa inna ilaihi raj’un” take ta nanatawa. Wani irin k’ara ta saki “Wayyo Allah! Anas... Anas ne mutumin, I married the man who raped me, I fell in love with the man who raped me, mutumin danata had’asa da Allah karya k’wace min budurcina amman yak’i koda tausaya min haka ya danne ni ya amshe min martaba. I married the man who made my life miserable, mutumin daya juya min rayuwa ya raba dani da first love d’ina AHAMD bawan Allan da yasoni tsakani da Allah, na auri mutumin da yayi sandanin rashin lafiyan mahaifina, mutumin daya jefa min rayuwa cikin k’unci da bak’in cikin rayuwa, mutumin daya sani cikin tsoro kowani dare sena tashi ina kuka ina mafarki ze dawo ya sake azabar dani kamar yadda yayi a baya. Innalillahi wa inna-” bata k’are salatin ba wani erin masifaffen kuka cike da azaba ya rufe ta, ihu take sosai wasu irin zafaffun hawaye suna ambaliya a fuskarta se juyi take kan rug d’in (k’aramin carpet) ji take kamar ranta ze fita, wannan wace erin rayuwa ce? “No this can’t be Ya Allah kasa mafarki ne wayyooo!! this can’t be happening mesa ban tab’a gane shine wanda yayi raping d’ina ba? Am I that stupid da har na fad’a soyayya da mugun mutumin daya cuceni har abada? Taya tun rananda naga wancan babban ciwon dake hannunsa na kasa gane a ina na tab’a gani? Taya nakasa recognising blue eyes nasa Why am I stupid?” Kai take kad’awa a yayinda kukan ta ya tsananta har wani sama sama nishinta yake tafi minti talatin tana kuka kamar wacce ta zare, idanunta sunfi jan kala shiga rabuwanta da tashin hankali irin wannan tun lokacin da abin ya faru. A sannu a sannu ta rarrafa wajen drawer’n ta miyar masa da littafin ciki har ayanzu kuka take ba makawa da k’yar ta ja kanta d’akinta tasa key ta rufe sannan ta baje kan gado, d’aurin kan nata ta sinche tasake k’urma wani irin balad’ad’d’en ihu tana jan bedsheet na kan gadon tana duk’unk’unewa a hannunta. “Anas mesa zaka min haka? Mena maka? Mesa seni? I thought I could trust you Anas why does it have to be this way? Wayyo Allah wayyo kaina.” ta rik’o kanta dan wani erin ciwon fitan hankalin da yake mata. “I married a monster. Ya Allah tanan ka kamani akan qaryan danayi ma iyaye na nasasu suka amince auren soyayya mukayi da Anas? Ya Allah na tuba kayafemin badan hali na. This is a dream ba reality bane it can’t be it just can’t be.” Kuka Fannah ke kamar zata cire ranta har cewa take a ranta ina ma Allah ya d’auki ranta kawai ta huta dukda tasan yin hakan haramun ne, amma kuma da living irin wannan rayuwa gara mutuwa, bayi ma Allah shisshigi ba amman mesa rayuwarta take haka? Daidai lokacin data sama wa zuciyarta sukuni ta fara son Anas hakan ze faru why? Why? Kuka ta cigaba da yi ciwo kanta yake mata kamar ze tsage amman still tak’i barin kukan tun hawaye na zuba har hawayen nata ma yayi seizing, shima muryan nata ya d’auke dan irin ihun data riga yi amma haka tacigaba da kukan ba sauti saboda rashin tausayawa kanta. Wannan wace erin jarabawa ce? Ka auri mutumin da yayi raping naka ba nan kad’ai ba har ka soma son meshi. Wace erin k’addara ce haka? “Zama na a gidan nan ya k’are barin iya cigaba da rayuwa da mutumin daya rabani da farin cikin rayuwa naba, barin iya cigaba da rayuwa da kai ba Anas.” Murmushin takaici ta saki “mesa ma nake son sanar dakai sirrina bayan kafi kowa sani? Bayan kafini ni karan kaina sanin wannan sirrin, nayi sakaci da sallolin dare da addu’o’i na shiyaza har na aureka ban gane kaba. Anas abinda kamin is UNFORGIVABLE ka dawo ka sallameni kawai inkuma barakayi ba in tattara kayakina inbar maka gidanka I can’t continue living you with Allah kad’ai yasan abinda zaka iya min nan gaba.” _4:21PM_ Daidai nan Anas yake dawowa daga office cikin jin dad’i ya miyar da k’ofar ya rufe, he can’t wait ya sa Flowersa a ido. Flasks yaga suna masa sallama kan dining table wanda kobe bud’e ba yasan favorite nasa ne ciki ba abinda yakeyi aransa banda sawa Fannah albarka besan ya rayuwarsa zata kasance ba Flowersa ba. Kitchen yauma yasoma lek’awa beganta ba daga chan yayi d’akinsa. Murmushi ya saki danko yanada tabbacin a d’akinta take. Bayan ya rage kayan jikinsa ya nufa d’akinta sede tun daga nesa yakeji kamar sautin kukan mutum... Kukan mace... Kukan Fannah OMG! “Flower” a rikice ya kira sunanta ya k’arisa k’ofar d’akin ya gwada bud’ewa suprisingly yaga a rufe da lock. Tana jin k’ara ta miyar da kallonta kan k’ofan. “Fannah! Fannah! Open up please mesa kike kuka? Dan Allah stop it kitaso ki bud’e min k’ofan please.” Kukan nata ne ya tsananta daga jin muryarsa. “OMG! Fannah whats wrong? Why are you crying dan Allah ki bud’e” yayi stating cike da tashin hankali bare iya jure kukan flowersa ba meya sameta? Meyasa take irin wannan matsanancin kukan? Bubbuga k’ofan yake da k’arfin da Allah yabasa amman yakasa b’alla gun lock d’in dake security door ne. Tana tsugune a k’asa se kuka take sha kamar ba gobe. “Dang it!” Ya buga k’ofar a fusace se a yanzu ya tuna da akoi spare key a 360 ya wuce d’akinsa yaje ya binciko ya ciro da sauri ya dawo yasa ya bud’e k’ofar. Da gudu ya nufi k’asa inda ya ganta ko d’ago kai ta kalle sa batai ba tsugunawan yayi shima a gabanta cike da tashin hankali da tsantsan tausayi. “Flower” ya kira sunanta cikin sanyin murya cike da tausayi. “Flower dan Allah kibar kukan nan please ya isa dan Allah” ya sanar da ita muryarsa har shaking yake dan tausayi. Ko d’ago kai ta kallesa batai ba se kuka take ba makawa hannu yasa ya dafe kafad’arta hannunsa na tab’a ta ta d’ago kai a firgice ta matsa baya sekace taga aljani. Beso sake ganin fuskarta ba dan yadda ya kumbura gakuma wani irin mahaukacin jan da idanunta sukayi besan seda idanwansa shima suka cike da hawaye ba. “Fannah why are you crying like this? Meya sameki?” Hannunta ya gwada rik’ewa a firgice taja baya tana matsawa baya daga garesa ganin haka yace, “Fannah Anas ne ba mutumin ba, kinji?” gabad’aya yagama zato ko mafarkin mutumin data sabayi ne tayi take irin wannan wahalallen kukan. Kai kawai take girgiza masa. “Its me Anas your husband bawani ba come kinji?” kai ta kad’a masa ike da tsoro daga gawani irin kallon da take masa. A guje ta ruga bayi tasa key ta rufe a gujen shima yabi bayanta cike da tashin hankali. “Fannah meya faru dan Allah?” Jikinsa ne ya soma basa ba mafarki tayi ba to mene neh? Ko rasuwa akayi mata? Amman ai in rasuwa ne da shima za’a kirasa a sanar dashi. “Fannah I beg of you dan Allah kibud’e please.” Sautin kukanta ta tsananta tana tsugune k’asan bayin se kuka take kamar zata cire ranta. K’ofar yake ta bugawa ba yadda beyi ba dan b’allawa amman ya kasa besan lokacin da hawaye tsili-tsili suka soma gangaro masa kan kumatu ba. Da kukan Fannah ya gommaci yarasa duk wani abinda ya mallaka a duniya. Daga k’arshe ma kasa rik’esa k’afafunsa sukayi sauk’a yayi har k’asa hannun sa dafe jikin k’ofar “Fannah koda baraki bud’e k’ofan ba please kibar kukan dan Allah kibari I can’t take it please I beg you.” Har ayanzu batajin zata iya dena kukan ba. “Fannah dan Allah fa nace kibar kukan please ya isa haka nasan kinada qwararran dalilin dayasa kike haka becuase I trust you Fannah and I love you please come out kinji? Barin bar nan ba sena gankin Flower” ba irin rok’ar duniyan da be mata ba amman sam tak’i bud’e k’ofar. Ga wani irin masifaffen yunwan dake cinta rabuwanta da abinci tun breakfast gara shi Anas d’in yachi lunch a office. Har Maghrib suna nan ahaka ganin lokacin Sallah ya shiga yayi k’arfin hali yace, “Fannah kifito kiyi Sallah kinji? Nasan koda zan had’a sama da k’asa bara ki bari in ja muba so kifito kiyi naki nima zanje inyi nawa, I love you.” Yana kaiwa nan ya fice seda ta jiyo k’aran rufe k’ofa sannan ta dage ta yi alwala har wani dashi dashi take gani dan ciwon kai dakuma tsantsan yunwa. Cike da tsoro ta bud’o k’ofan bayin kad’an ganin baya cikin d’akin ta d’an taka da wuri ta zaro spare key ta bayan k’ofar ta sake locking abinta yadda bare iya shigowa ba again. Yin Sallan kawai take badan tasan me take karantowa ciki ba dan tashin hankali ko raka’a uku tayi ko had’u tayi bata sani ba se Allah shima Anas ta b’angaren sa haka ne. Yana sallamewa ya d’ibi hanyansa back to d’akinta nanma yaga ta kuma rufewa gashi ta zare spare key d’in. Kai gaskia ba lafiya ba what is wrong with Fannah? why is she acting thsi way? Ko an mata wani abu ne? The real question is ko nine na mata wani abu bisa rashin sani. Tsayawa yayi yana nazarin abubuwa sam bai tunanin da akoi aami abinda ya mata wanda za’a ce shi yayi hurting feelings nata haka. Barin maganar zucin yayi a haka “Fannah nasan kina jina I don’t know what got into you sabida ban tab’a ganin ki a yanayi irin na yau ba ko abinci kink’i chi tun d’azu nake miki magana amman kink’i tankani I can’t take it anymore. Please in wani abun na miki wanda yayi hurting naki haka I’m sorry kiyi hak’uri dan Allah ki sanar dani na zauna nayi tunanin duniyan nan amman na kasa tuna koda abu d’ayan dana miki da zesa ki shareni haka yau har ki rufe kanki a d’aki. I’m sorry I’m truely sorry ko abinchi ne kifito kichi not for my sake but for your health’s, I love you.” Ya sanar da ita cikin cracky voice yana kaiwa nan ya wuce d’akinsa ko maybe intaji alamun ba motsinsa zata fito. Kalamunsa masu narkar mata da zuciya taji bata k’aunar sake sauraronsu ko k’arfin kuka batada. 20 minutes later bayan ta tabbata baya bakin k’ofar ta mik’e tana dafe dafe har ta isa bakin k’ofar ta bud’e a hankali, leqawa tayi da kyau bata ganshi ba sannan ta sa kai tajeta dining area ta d’ibo abinci kad’an kan plate ga yunwa har yunwa amman ba tajin zata iya chin abincin ma. Ruwa ta cido daga fridge d’in takama hanyan komawa d’akinta gabanta ne yayi mumunan fad’i ganin Anas da tayi tsaye jikin k’ofar d’akinta, data kallesa seta gano yayi kuka shima. Toh kukan meh kuma zeyi bayan abinda ya mata shekaru had’u koma tace biyar da suka wuce. Kai ta soma kad’awa take hawayen ta da sukayi seizing suka soma sauk’owa. A hankali take ja da baya baya wane taga aljani. “Fannah please why are you doing this?” Ya tambayeta cikin wani irin salo. “Mesa Flower? Meya faru? In ni na miki wani abun I’m sorry dan Allah ki sanar dani mistake nawan se in gyara kefa kike cemin a baya silence is never the solution to a problem amman kuma kikeyi yau please talk to me.” Kai still take kad’a masa ga wani irin b’arin data soma yi hawaye se ambaliya suke kan kumatunta. Taku ya soma yana nufanta. Takasa furta koda ‘A’ se baya baya take har ta isa jikin bango bebar binta ba alokacin da ya rage saura befi taku uku tsakaninsu ba nishinta ya soya tsabagen b’arin da hannunta suke batasan lokacin da ta sake plate da gorar ruwan a k’asa ba. “Tata tas!!” kukeji k’aran fashewar glass. *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:57, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 7⃣0⃣ Miyan kap jikinta ya zube shima Anas yad’an tab’a sa kad’an. Irin rikicewa da b’arin da Fannah keyi ko gamo mutum yayi da aljan bareyi irinsa ba take ta tsuguna tasoma tattarawa abinda Anas ya tsana kenan ya washi yaganta tana picking broken glasses da hannu. Kafin yace tabari ko ya d’aga ta aikin gama ya riga ya gama kyat! Ta yanke a yatsanta k’ara sosai ta saki kamar a kyaftawan ido ya k’ariso gabanta hannayensa na sauk’a akan jikinta ta tsala wani irin rikicaccen ihun da shi kansa seda ya firgita. “Fannah please what is wrong with you? Anas nefa ba wani ba, its Anas your husband mesa kike haka da zaran na tab’aki ki rikice? Muga hannun” da zaran ya matso ze tab’a ta seta sa ihu ko magana takasa masa duk tabi ta tsure ta gefensa tabi da gudu da sauri ya cafko ta da hannu ya dawo da ita baya. “Fannah what is your problem why are you acting like this? Mena miki kike gudu na kamar kinga mala’ikan d’aukan rai, what is it tell me?!” Ya k’are maganar cikin sautin tsawa saboda he can’t take it anymore taya matarsa zata na gudunsa haka. Hannun nata take ta k’ok’irin fisga amman takasa hawaye kam sekace lalacaccen famfo. Bright blue eyes nasa da suka zamanto dull and weak dan tsantsan tashin hankali ya d’agosu a maraice yana kallonta se k’ok’arin karb’an hannunta take amman takasa. “Fannah mena miki? Ki fad’a min please, OMG!” Yayi exclaiming alokacin dayaga yadda jinin jikinta ke zuba a k’asa. Hannunta yasoma ja zuwa d’akinsa. Sam tak’i bud’e baki ta masa magana se hawayen da takeyi ganin sunkusan kai ga d’akinsa ta ja hannunta da k’arfin da Allah yabata seda ta fisge daga rik’onsa. “Fannah please don’t go…” bata ko sauraresa ba ta ruga d’akinta a guje tare da sa lock. Har k’asa ya sauk’a wasu irin zafaffun hawaye na maza suna sauk’owa tsili-tsili a fuskarsa. “Why Fannah? Mena miki? Your silence is killing me why are you punishing me like this?” Itama Fannar ba abinda take banda kuka, wanke ciwon nata tayi se kuka take ga wani irin yunwan dake azabartar da ita batajin zata iya kwana inbatasa wani abu acikinta ba. Rarrafawa tayi zuwa fridge na d’akin hamdala ta saki ganin da akoi cookies da drinks uku ciki. Ledar cookies d’in ta ciro ba makawa ta soma kaiwa cikinta seda taci fiye da rabi sannan ta kora da fanta nan ne tad’anji dama-dama. K’aran shigowar sak’o taji a wayarta kamar wacce barata duba ba sekuma ta miqe ta bud’e taga saqo ne daga Anas ta karanta kamar haka; _Fannah please in wani abun na miki ki sanar dani stop punishing me like this zuciyana bare iya d’auka ba please Flower I’m missing your smile, body, and fragrance already open the door for me please. I love you #crying_ Wani sabon kukan ta fashe da har k’asa ta sauk’a tana birgima a kan rug na d’akin. Anas dake bakin k’ofar ji yake kamar ya b’alla k’ofar yashiga if only he could. “Fannah please stop crying kinji dan Allah kibari... Kidena please stop it” yayi stating cikin sautin kuka. Zama yayi bakin k’ofar yana hawaye tana kuka. Isha nayi ya rok’eta da ta tashi tayi Sallah ba gardama ta d’au hijabin ta tayi Sallan kamar yadda shima yayi a parlour bayan yagama shafa’i da wutr nasa ya dawo. “Fannah kifito kichi abinci kinji? I get it bakison sake sani a ido, zan koma d’aki sekin gama infito kinji? I love you.” Yana kaiwa nan ya juya a sanyaye kamar wanda k’wai ya fashe mai a ciki ya nufa d’akinsa bayan minti ishirin ta bud’o d’akinta a hankali, parlour ta nufa dan tattara wajen da plate ya fashe mata d’azu to her suprise taga wajen tsaf ko alaman miya babu tsaf Anas ya share yayi mopping. Dining area ta nufa ta d’iba abincin kad’an se sauri take kar ya fito su had’u gefen flask d’in taga wani paper hannunta na b’ari ta d’aga ta karanta. _Flower please wear the plaster and cover your wound please kinji? I’m sorry._ Wani sabon kukan taji yana k’ok’arin rufeta ga plaster’n tana gani amman batajin zata iya d’agawa, miyar da paper’n tayi ta ruga d’akinta a guje ta baje kan gado, ta cigaba da kukan daga inda ta tsaya. Bayan shiganta da kamar minti uku Anas yafito daga d’akinsa wajen daya ajiye mata paper’n ya nufa disappointedly yaga bata d’aga plaster’n ba to ko bata fito bane? Flask d’in ya bud’e yaga da alaman ta d’iba abincin mesa bata d’au plaster’n toh? “Fannah haka kika tsaneni yanzu? Bakiya son koda help d’ina?” Ya k’are maganar da hawaye na gangarowa daga kumatunsa guda. Hannu yasa ya share ya koma bakin k’ofar d’akin ta ya zauna yana sauraron sautin kukanta yana hawaye shima har bakin sa yayi dogo da ce mata tayi shiru amman tak’i. K’arfe 9:00PM na bugawa ya mik’e “Fannah anan zaki kwana?” Ya tambayeta tana jinsa amman tak’i amsawa dan batada burin sake masa magana a rayuwarta again. “Fannah kifito muje mu kwanta kinji? I can’t sleep without you by myside please kifito.” Sautin kukanta yaji ya k’aru. “Flower kibar kukan nan please...” ba irin rok’ar duniyan da be mata ba amman tak’i bud’e k’ofar ta kuma k’i barin kukan, ga wani uban ciwon kan da ke cinta. D’akinsa ya koma ya d’ago pillonsa da bargo ya dawo bakin k’ofar d’akinta ya shimfid’a ya kwanta kai be damu da uban sauron Maiduguri ba all he knows is that he don’t want to leave his flower alone. “Fannah goodnight, I love you so much.” Alokacin da yayi maganan tana kwance kan gado ta d’au tafiya yayi wani irin tsoro taji ya ratsa ta ko kashe wutan d’akin ta kasa, duk’unk’une kanta tayi cikin bargo se b’ari take cike da tsoro. Tafi awa d’ai tana neman bacci sannan a wahale yazo mata. Anas kam sam ya kasa bacci he is missing her in his hands se juyi yake amman ya kasa bacci bare iya kwatanta how he is missing her legs wrapped around his body ba. ***** 2:34AM Firgit Fannah ta farka dan wani erin masifaffen mafarkin datayi. “Anas!” ta kira sunansa da ihu take ya jiyota dake daman baccin nasa beyi nisa ba. “Fannah” ya kira sunanta tare da mik’ewa. “Fannah I’m here kinji?” Kuka take sosai cike da tsoro duk ta duk’unk’une kanta da bargonta ta cusa kanta cikin cinyoyinta se kuka me sauti take. “Anas” ta sake kiran sunansa. “Yes Fannah I’m here please stop crying bud’e min kinji please I beg you...” Har a yanzu bata bar kukan ba. Zaman gadon ne ya gagareta ta tako zuwa bakin k’ofar ta tsaya adaidai lokacin yake kiran sunanta again “Fannah.” Kuka ta fashe da, yana jin muryarta kusa dashi hankalinsa ya sake tashi. “Fannah, Fannah ki bud’e min kinji? Let me in please.” Kuka take sosai ta inda yakejin sautin kukan nata ya matso tare da had’a kansa da wajen “Fannah I’m here please kibar kukan.” K’asa ta sulale kamar yana ganinta shima ya sauk’a. Hannunta ta aza jikin k’ofar tare da dafe kanta jikin k’ofar tana me cigaba da kukan. Daidai inda hannunta yake ya aza nasa shima “Flower I’m here you are not alone I’m here with you kibar kukan kinji?” A hankali taji tsoronta na gushewa da dad’ad’d’un kalamun Anas awajen bacci ya d’auketa tun Anas najin k’arfin nishinta har yazo yaji shiru hakan ya tabbatar masa tayi bacci anan ne shima yasamu ya d’an kwanta although sauro sunk’i barinsa saura na masa waqa a kunne saura suna cizon sa farin fatarsa duk yayi pink amman haka ya hak’ura dan baison barin Fannah ita kad’ai ahaka har Asuba tayi bayan ya idar da nasa ya gama addu’o’insa ya dawo ya soma kirar sunanta a hankali cikin baccin tasoma jin sunanta. “Fannah ki tashi kiyi Sallah kinji? Asuba yayi. Fannah tashi kinji?” A kasalance ta mik’e ta nufa bayi ta d’auro alwala tayi Sallah sannan ta koma kan gado ta kwanta har a yanzu Anas ya kasa bacci. Ko kad’an baijin ma ze iya zuwa office yau, bare iya barin Fannarsa awannan hali ba. Se anan ne yasamu yayi bacci shima 9:45AM ya tashi har anan Fannah na bacci tattara bargon nasa yayi ya wuce d’akinsa yayi wanka sannan yayi shirinsa na kullum fridge ya dosa ya ciro irin sliced potatoes d’innan da ake packaging ya musu frying da omalet ya had’a musu breakfast. Cikin awa d’aya dining table is set agogon hannunsa ya duba yaga 11:02AM knocking yaje yayi a k’ofar d’akinta alokacin da take fitowa daga wanka kenan. “Fannah kin tashi? If yes good morning kifito ki karya kinji? I love you” yana kaiwa nan ya koma dining ya soma zaman jirarta. Kukan dake son k’eto mata ta shanye simple doguwar riga tasa bak’i me silky jiki. Babban akwatinta ta ciro ta soma tattara kayakinta wanda zatayi amfani dasu ciki. Dam ta cika da essential stuffs nata ba mantuwan da tayi tana gama had’a akwatin ta ja ta rufe sannan ta zira hijabinta dogo har k’asa ta d’au wayarta sannan ta soma ja, a hankali ta bud’e k’ofar ta fito tafiya take kanta a sunkuye da jakarta tana ja daidai ta iso parlour ta bayyana a idon Anas. Kasa believing abinda idanunsa suke gane masa yayi. What is he seeing? Ina Fannah zataje da wannan babban akwati? Ganin se dosan bakin k’ofa take ya k’urma mata kira “FANNAH PLEASE STOP!” A guje ya nufa inda take, k’ara saurin tafiyar ta take gabanta yasha da wuri idanunsa take suka kad’a sukayi ja. B’ari bakinsa yake kalamunsa suna stammering “Fa.. Fan.. Fannah meh wannan? Ina za kije? Meke faruwa Fannah? Tafiya zakiyi ki barni? Mena miki Fannah? Dan Allah karki tafi in wani abin na miki tell me I’m sorry for everything that I’ve done I’m sorry please karki tafi.” Ya k’are maganar cikin sautin kuka. Zuciyarta taji ya karye, batasan seda hawaye suka soma ambaliya a fuskarta ba sam ta kasa dena kukan musamman ma dataga alaman cizon sauro all over his face and hands nufin a waje ya kwana yana gadinta jiya. “ Fannah please karki tafi mena miki da zaki tafi? Kiyi hak’uri dan Allah.” Hannunta yayi yunk’urin rik’ewa baya taja da wuri taja akwatin nata tabi ta gefensa da wuri ya rik’o hijabinta. Abin da be tab’a faruwa ba ya faru yau. Mr. Fauzi ya sauk’e girman kai da duk wani feeling daya keyi ya sauk’a har k’asa akan knees nasa duka biyu. Hawaye yake sosai “Fannah please don’t go dan Allah karki tafi. In wani abun na miki please let me know.” A nitse ta juyo ganinsa akan guiwowinsa ba k’aramin mamaki ya bata ba. Idanunsa a raunane ya d’agosu yana kallonta duk setaji wani iri tasa mijinta kneeling tace masa ya tashi kuma batason sake masa magana ganin yadda yake kuka itama ta k’ara k’arfin nata kukan. Juya masa baya kawai tayi batason ganin hawayensa kamar yadda shima baison ganin nata. “Fannah turn and look at me please mesa zaki tafi? Mena miki? Kinsan barin iya rayuwa ba ke ba please karki tafi Fannah in wani laifin na miki ki sanar dani dan Allah.” Juyowa tayi cikin sautin kuka ta soma magana har wani sama sama nishinta yake. “Anas are you serious? Bakasan me kamin ba? Kana nufin har a yau baka gane ni ba? Kana nufin baka san yarinyan dake *_TARE DA KAI_* ba har a yau?” Cike da rashin fahimta ya taso “Fannah what are you talking about? Wace yarinya kike nufi?” Hannu tasa ta share hawayenta kamar yadda yayi shima. “Anas kaine mutumin, kai nake mafarki kullum zaka dawo ka sake azabartar dani kamar yadda kayi 5 years back. Anas don’t you get it? I’m the girl, nice yarinyan... Ni kayi raping 5 years bacm. Nice yarinya from the incident a Bama na yammacin Asabar 23rd of March...” Sekuma ta fashe da wani irin masifaffen kuka. K’wak’walwarsa kasa d’aukan abinda ke faruwa yayi. Se kai yake kad’awa yana salati a ransa da k’yar bakinsa ya bud’u cike da tashin hankali da rashin yarda yace “no you are not Fannah, you are not the girl inda kece da nayi noticing naki bake bace Fannah baki gane bane taya ma kika sani? I never told you.” “It doesn’t matter ‘cause I read your diary Anas ni kayi raping. Anas nice yarinyan da ka raba ta da budurcinta, ka cuceni Anas saboda kai nida family na muka bar Bama muka bar ‘yan uwanmu, saboda karya me bin maza da ‘yan unguwa ke kirana dashi muka bar Bama a sanadin abinda kamin, saboda abinda kamin Anas ka rabani da first love d’ina AHMAD wanda yasoni tsakani da Allah, saboda kai na rasa gatana, sabida kai Ya Farouq da Baffah Khaleel suka samu baki suke zagina suna kirana karuwa saboda abinda kamin kasa Baba ya kamu da ciwon zuciya Anas you are the source of my sorrow and fear. Mena maka Anas? Mena tab’a maka daka gommaci ka k’untata min? A rayuwa ba abinda naso kamar in gyara maka rayuwarka and I did mesa ni baka min haka ba? Mesa ka shafawa rayuwata bak’in fenti Anas? Barin iya zama dakai ba, barin iya cigaba da zama da mutumin daya cuceni kamar yadda kayi ba. Ka sallameni in tafi gida ka sallameni inkoma gun Mami na dan Allah karka hanani takarda na. Anas I’ve loved you but not anymore, I thought I could trust you why is the handsome Anas I know turning into a monster? Ka sallameni dan Allah...” *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:57, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 7⃣1⃣ Kai yake kad’awa cike da tashin hankali a yayinda zuciyarsa tak’i amince masa da abubuwan da Fannah ta fad’i masa, hawaye yake sosai abin tausayi sam yakasa koda bud’e baki yayi magana because of how shocked he is. Ina ma ace ba’a tab’a qaddara masa wannan rana ba, mesa se Flowersa? Nufi kenan itace yarinyar data ta had’asa da Allah karya mata abin amman ya mata? Just how much pain have he made her gone through? Itace yarinyan datake fito masa kullum a mafarki tana ce masa *_TANA TARE DA SHI_* there’s nomore denying Fannah ce yarinyar mesa betab’a noticing nata ba? Why? Sede a sosai yanajin yatab’a saninta wani wajen amman baya iya tunawa. Da k’yar bakinsa ya iya bud’uwa cikin wani irin murya cike da nadama yace _“Fannah... Fannah I... I’m so so sorry dan Allah kiyi hak’uri Fannah kece yarinyan kece ita, kece yarinyan danayi taking advantage naki Fannah bansan ta ina zan soma baki hak’uri ba, raping naki danayi shine BABBAN KUSKUREN DANA TAFKA (littafin rash kardam) if only I can tell you how sorry I am danayi. I’m sorry for everything that I’ve done, I’m sorry for breaking you precious heart. Fannah barin iya baki hak’uri ba tun rananda abin ya faru nasoma living a life full of guilt tun daga ranan nakasa samun sukuni kullum cikin tunani da mafarkin ki nake. Fannah please karki tafi ba’a cikin hankali na na aikata abinda na miki ba I was drunk that evening takaicin abinda Ummimi ne duk ya sani I needed someone to blame it on sekuma Allah ya kawoki path d’ina. Fannah wannan k’addaran ba naki kad’ai bane I know you’ve suffered morethan alot amman kisani nima I did wallahi I will do everything I mean everything inga kin yafemin. Fannah I was just 18 nayi wrecking naki I was young and stupid kema kinsani barin tab’a aikata abin danayi da a baya ba yanzu, kisani ba’a son raina na rabaki da martabarki ba, Fannah ba’a son raina na rabaki da Ahmad, kamar yadda ba’a son raina nasa Baba yakamu da ciwon dayake fama dashi ba dakuma saku barin ‘yan uwanku a Bama. Fannah kece yarinyan danayi spending shekara da shekaru ina nema saboda in nemi gafararta...”_ Matsowa kusa da ita yayi ganin zatayi baya ya dakatar da ita sake sauk’a yayi kan guiwoyinsa ya ajiye duk wani girman kai da feeling nasa a gefe. A raunane ya d’ago idanunsa ya azasu kan kumburarren fuskarta da hawaye ke ambaliya kai. _“Fannah please forgive me dan Allah ki yafemin I’m so so sorry for breaking you heart for making you go all through those meseries, dan Allah kiyi hak’uri nasan banida right na neman gafararki but nasan kinada pure and good heart ki tausayamin kiyafemin please I’m sorry for everything that I’ve done to you, Fannah inda zan iya reversing time in miyar da komai normal da nayi, abinda ya faru ya riga ya faru mu d’ausa as k’addarar a rayuwanmu Fannah I don’t want you to leave please stay with me kamar yadda kikecemin a kullum_ *_KINA TARE DA NI_* _prove it to me. I will never hurt you Fannah this I promise. Wallahi ban tab’a son wata macbayan keba Fannah bame matsayinki a zuciyana koda kuwa Amal ce banida kamarki ki tausaya min karki tafi dan Allah..._ ya k’are maganar cikin hawaye. Sosai ta tausayawa Anas kalamunsa ba wanda be kwanta mata a rai ba, tana son Anas tana sonsa sosai amman batajin zata iya yafe masa abinda ya mata... Aduk lokacin data tuna da irin azaban datasha alokacin dayayi forcing kansa cikinta cike da azaba da rashin imani ko tausayi setaji barata iya yafe masa ba dukda kuwa a bige yake a lokacin amman still hakan be basa daman yayi raping duk wanda yagani kan hanya ba. Hannu tasa ta share hawayenta har a yanzu idanun Anas basu bar kanta ba ya zura mata jajayen idanunsa yana jiran amsarta yana nan a kneeling position d’in har yanzu. “Anas dan Allah ka tashi stop kneeling infront of me, katashi please” “Fannah har senaji kin yafemin baraki tafi ba zantashi kiyu hak’uri please.” Muryarta daya dishe dan kuka tayi clearing sannan tasoma kamar haka; “zama na dakai ya k’are Anas. Batun yafiya kuwa zan yafe maka Anas saboda d’an Adam ajizi ne musamman ma danasan labarinka nasan duk wani abinda ka aikata na haramun Ummimi ce sanadi ga kuma yadda ka tuba, na gamsu da tubar dakayi. Zan yafe maka duk wani abinda kamin Anas amman hakan bawai yana nufin zan cigaba da zama dakai bane tafiya yazamo min dole ka sawwaqe min please.” Hijabinta ya tattara ya rik’e a hannunsa yana hawaye “Fannah karki min haka dan Allah ki dena fad’in zaki tafi, kina nufin kin tafi har abada baraki sake dawowa ba kenan? Ya kikeson in rayu? Fannah wallahi da in rasaki gwara in rasa komai koda kuwa raina ne wallahi barin iya rayuwa ba keba dan Allah karki tafi, I beg of you please Fannah nasan kinada tausayi baraki iya tafiya kibar masoyinki ba...’ ya k’are maganar hawaye na fitowa bibbiyu a idanunsa. “Anas dan Allah kadena” ta karb’e hijabinta “kace zakayi everything dan in yafe maka. Ka taimaka wa rayuwata ka sakeni dan Allah. Anas tsoronka nakeji I don’t know what you are capable of doing. Yafiya kace kanaso with time in shaa Allah zan yafe maka amman dan Allah karka hanani takarda na.” duk yadda tayi ta had’iye kukan ta kasa. “Fannah barin iya rubuta miki takarda ba barin iya sakan kiba, barin iya karya promise dana d’auka nacewa duk rananda Allah ya bayyano min ke zan kula dake ba I can’t let you go, I can’t lose you for the second time. Fannah wallahi I will never hurt you inda zanyi da na jima da aikatawa. Fannah can’t you see? Ko hak’k’i nama na tauye wa kaina just so as not to hurt you, tunda na fara sonki ki fad’a min abu d’aya wanda nayi yayi hurting naki, I love you morethan I love my own soul. Fannah tausayinki yamin yawa barin tab’a iya sakanki ba dan Allah kibar had’ani da Allah akan in baki takardan ki saboda I can’t kamar yadda I can’t say no to your offer anymore.” “Anas in baraka bani takarda na ba zan tafi, Allah k’ara mana hak’uri dukan mu I wish you farewell. Thank you for all the help daka min right from day 1 na had’uwan mu barin tab’a mancewa dasu ba, kasani I’ve loved you and har in mutu kanada gurbi a zuciyata.” Tana kai nan taja jakarta ta juya besan lokacinda ya tashi yajata ta fad’a jikinsa ba. “Anas ka sakeni ple-” bata k’are maganar ba ya lalubo lips nata ya had’a da nasa yana mata wani irin kiss, kissing nata yake hungrily. Sam tak’i basa had’in kai ba abinda take se hawaye tana ta shuresa amman kaman maye yak’i hak’ura sam yak’i giving up seda ya tabbata ya kashe mata jiki dakanta tabar bugin da take masa tabasa free passage. Hannunsa ya zagaye akan ‘yar kunkumin nata yasake matso da ita jikinsa itama a hankali ta zagaye hannayenta a wuyansa sun d’au tsawon lokaci suna abu d’aya. Suyi su tsaya suyi gasping for air su cigaba se chan da yayi pulling out ta manna goshinta a hab’arsa ta soma hawaye. Hugging nata yayi gagam har yana affecting mata numfashi. “You can’t go Fannah, wallahi barin iya rayuwa ba keba, punish me kimin duk wani abinda kike ga ya kamance ni Fannah inma kotu zaki kaini ki kaini amman dan Allah don’t leave me, don’t ever please. I love you, I love you Flower don’t leave me please. Abinda ya faru ya riga ya faru tafiyarki will not solve anything kizauna muyi magana please you’ve changed me banason tafiyarki ya kuma canzani.” *D’an sanarwa please masu karatu in kun kura zaku ga page d’innan yayi gajere compared to sauran. Kamar yadda wasunku suka sani inada ciwon baya kuma akwana biyun nan danake yawan zama ina typing seya k’aru saboda haka likita ya buk’aceni da in rage zama saboda haka zaku d’an jini shiru na kwana biyu haka, ina me baku hak’uri, I love you all* *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:58, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: Miemiebee Novels › Home View web version Tuesday, 13 September 2016 Mariam Anass at 12:28 TANA TARE DA NI... TANA TARE DA NI... PAGE 72 BY MIEMIEBEE Wani irin wawan mutuwa jikinta yayi ga kuma wani erin tausayin Anas daya kamata lokaci guda mara misantuwa. Kasa ce masa koda uffan tayi, alokaci d’aya k’wak’walwarta ta toshe, ta rasa me zatayi ta zauna ne kokuwa ta tafi? Kalamunsa duk sunbi sun kamata batason tafiyarta ya kuma canza mata shi ya koma gurb’arcacciyar rayuwarsa na da. In hakan ta faru barata tab’a iya yafe wa kanta ba. Hawayen da suke gangarowa kan kumatunta se k’aruwa suke a yayinda zuciyarta ke k’ona in ta tuna ta auri mutumin daya jefa mata rayuwa cikin k’unci, worst part d’inkuwa shine irin zazzafar soyayyar da take masa wanda bata zaton ta tab’a yima wani mahaluk’i ba, soyayyar da bata tsammanin akoi takwabin daze iya kashesa tasani ba na mijin da ze zauna da ita da mutunci kaman yadda Anas zeyi aduk fad’in duniya tunda gashi da gaskia ya bayyana ma ya nuna yana sonta kuma ze cigaba da zama da ita still kuma koba dan haka bama tunba yau ba yake bata labarin yarinyan cewa duk lokacin da ya sameta zeyi all he can ya yafe mata amman ita batajin zata iya cigaba da zama dashi saboda abin da zafi kuma da ciwo. Sun d’au tsawon lokaci suna ahaka sam Anas yakasa sake ta k’ak’am ya matse ta jikinsa wane za’a k’wace masa ita, itako takasa hugging nasa back tana manne kawai a jikinsa se chan a hankali ta zagaye hannayenta bibbiyu a bayansa duk suna feeling turaren jikin junansu me tafiyar masu da imani, hugging juna suke cike da so da k’auna kowannen su na fatan ina ma ache wannan moment will last forever. Cikin sautin kuka ta kira sunansa. “Anas.” Kamar me jira takirasa ya amsa “na’am Fannah.” “Anas promise me baraka sake tab’a giya ba.” Bayanta yake shafawa, “Fannah anything for you I’ve promised you before and zan sake yau barin sake tab’a giya ba in shaa Allah I promise please don’t go.” “Promise me baraka sake firing workers naka ba” “Flower barin k’ara ba I promise.” “Promise me baraka sake aikata wani aikin haramun ba” “Flower I promise.” nanma yace. “Thank you” ta fad’a a hankali. “Does this mean zaki zauna dani? Baraki tafi kibarni ba?” Da k’yar ta iya ta raba jikinta da nasa ta d’ago jajayen idanunta da suke tsiyayar da hawaye har ayanzu ta kafasu kan fuskar Anas sosai shima idanun nasa suka kad’a hannu yasa ya share mata hawayen ‘yar murmushi tasaki masa sakamakon hakan wanda yasa yaji sanyi sosai aransa. “Fannah I love you so much.” Hannun sa ta sauk’e daga fuskarta a hankali tana murzawa sannan ta d’au d’ayan hannunta ta aza a nasa fuskar. “I love you too, I love you so much Anas.” Ta miqa kai tayi pecking nasa a kumatu. “But I have to leave” kamar a kyaftawan ido taja jakarta ta juya. Sauri sauri take ta bud’e k’ofar ta fita. “Fannah!” Ya kira sunanta da k’arfi cike da tashin hankali tare da shawo gabanta. “Fannah you musn’t go dan Allah ki zauna please.” Hawaye ya ke sosai kamar yadda itama take sam batason tafiyar dan de batada wata mafita ce a tunaninta. “Anas dan Allah karka hanani tafiya inhar kanaso na kamar yadda kake fad’a let me go please.” ta sanar dashi tana k’ok’arin shanye kukanta tare da bin gefensa, hijabinta ya riqo “I can’t let you go Fannah barin iya rayuwa ba keba dan Allah kiyi hak’uri niko da barakina min magana ba but please don’t go stay with me.” K’arfin hali tayi ta fisge hijabin nata dayayi yunk’urin sake tab’ata ta tsawata masa “DON’T TOUCH ME ANAS! DON’T!” mutuwan tsaye yayi a wajen yana hawaye kamar ba gobe yana kallonta tana jan akwatinta har ta fice masa daga kallo. “Fannahhhhh pleasssseeeeeee don’t gooooo...” yana sauk’a k’asa yayi wannan magana kuka yake kamar d’an yaro abin tausayi. Tana fita tasamu adaidaita sahu ta shiga ciki ta tsaya kuka kasa koda fad’a masa inda takeso ya kaita tayi tafi minti ishirin zaune ciki tana kuka sannan da k’yar ta sanar dashi a sannu sannu yakaita har gaban gidansu d’ari biyar ta dank’a masa ba tare da ta jira amshan chanjinta ba. Tana shiga ta tarar da Mami da Afrah da alama sun dawo daga rakiya ne. Mamaki ne ya mamaye fuskarsu duka ganin Fannah da akwati ba saqe-saqen da basuyi ba daga bisani Mami ta nufa bakin k’ofar ta rik’o Fannah ganin jiri nason d’ibanta, Afrah che ta amshi akwatin nata sukayi da ita d’aki. Har a yanzu ba wacce ta iya tambayar Fannah meke tafe da ita duk hankalinsu yabi yanayin datake ciki. Wani erin nishi take da inta ja d’aya ciki kamar na mutane goma sosai Mami ta tsorata ba kamar Afrah dake kuka already. Hijabin jikinta aka tub’e mata tare da k’ure fankan d’akin. Se anan bakin Mami ya bud’u “Habibti kukan ya isa dan Allah ya isa haka kinji? Yi shiru” ta sanar da ita tana jijjik’ata da k’yar kukan ya lafa sekuma ciwon kai bayan tasha magani ta d’an dawo hayyacinta Mami ta zaunar da ita. “Fannah meke faruwa? Ya na ganki haka? Kimin magana Habibti.” Wani sabon kukan taji ya faso mata, kwantar da ita Mami tayi a jiki tana bubbuga bayanta “fad’amin kinji?” Ba yadda Mami batai da ita ba amman Fannah tak’i tanka ta se kuka ba sauti da take tayi, tabari akira Anas ma tak’i duk tasasu cikin rud’ani da kuma san jin meya faru tsakaninta da Anas ga dukan alamu ba lafiya ba. Se chan Mami ta tura Afrah waje ta zaunar da Fannah tata yi mata magana cikin wani irin salo tana rok’arta. Se anan bakin Fannah ya bud’u “Mami ina Baba?” abinda ta soma tambaya kenan. “Yayi tafiya zuwa Bama Habibti kinason masa magana ne?” Kai ta kad’a “Mami banason Baba ya sani dan Allah kiyi min alk’awari baraki fad’a masa ba kosu Afrah ma baraki sanar dasu ba kuma baraki kira dangin Anas ki sanar dasu ba suma wannan abu da nakeson sanar dake yazama tsakani na dake ne kawai banason wani ya sani” ta k’are maganar hawaye na cikowa a idanta. “Fannah na d’au alqawarin dukda bansan me kikeson fad’a min ba amman na d’auka barin sanar da kowa ba. Meya faru?” Hawaye na tsiyaya a idanunta tace, “Mami shine mutumin, shine...” sekuma ta fashe da kuka. Cike da rashin fahimta Mami ta d’agota daga jikinta “wani mutumi Fannah kuma waye mutumin?” “Mami shi, shine mutumin wallahi shine.” “Fannah ki kwantar da hankalinki ki sanar dani gwara-gwara” tasa hannu ta share mata hawayen nata. “Anas, Anas ne Mami shi ne mutumin.” Kai Mami take gyad’awa nufin tasoma fahimta. “Anas ne wani mutumi Habibti?” “Shine mutumin mafarki na, shine wanda yayi raping d’ina a Bama Mami shine silar komai” ta fashe dawani irin matsanancin kuka. Salatin Mami kawai ke tashi a d’akin kwanto da Fannah tayi a jikinta tana bubbuga bayanta tana fad’a mata dad’d’un kalamu sam takasa yarda da abinda takeji. Anas? Yanzu Anas dama shi yama ‘yarta kaca-kaca haka? Shi ya lalata wa Fannar ta rayuwa sannan kuma yazo ya aureta yanzu ya sako ta kenan komeh? Gaskia Anas yacika butulu. Seda ta tabbata kukan Fannah ya d’an lafu ta d’agota daga jikin nata. Cikin wani erin salo cike da tausayi ta kuma kwantar da ita a jikin nata tana bubbuga bayanta itama kukan taji na k’ok’arin fin k’arfin ta inta tuna kalar wahalar da Fannah tasha shekaru bakwai da suka wuce (masu karatu kuka lura zaku ga d’ayan wajen nasa 5 yrs mistake ne) yadda suka tsinceta kwance a walaqance. Kukan Fannah ne ya tsananta da k’yar tasamu tad’an rage kukan. Cike da tausayi Mami ta tambayeta “Fannah kin tabbata da hakan kuwa? Taya ma hakan ta faru? Had’uwanku da shi Anas d’in tun yaushe ace baki ganesa ba be gane kiba se yanzu? Anya kuwa Fannah ba b’atan kai kikayi ba? Ace yadda Anas yake da mutunci da hankali gakuma daga gida me mutunci yafito ace har yasan yayi raping mace? Habibiti anya kuwa?” “Mami wallahi shine...” Nan ta labarta wa Mami kap abinda ta karanta cikin diary’n Anas bata bar komai ba harda labarin Ummimi komai ta kwashe tabawa Mami dasu shaye-shayen da Anas yakeyi wanda bayayi yanzu sam bata bar komai ba. Mamaki ne yacika Mami sosai takasa koda furta ‘A’ duk wani haushi da takaicin datake ma Anas kuma gabad’aya taji ya koma kan Ummimi itace silar komai dukda kuwa shima Anas da nasa laifin amman Ummimi ce me babban laifi anan. Wace erin uwa ce? Ance Uwa Uwa ce amman ba’a sa jerin kalan su Ummimin Anas ciki. Talauci hauka ne? Taya zata tafi tabar ‘ya‘yan data tsuguna ta haifa taya zata k’yamaci abunda yafito daga jikinta? Aiga irin abinda ya haifo nan tasa d’anta yata aikata haramun ko kad’an bata ga laifin Anas ba laifin sa data gani na k’in tawakalli da qaddara, nak’in accepting faith nasa shine kad’ai laifin daya tafka ita bama wannan ba yanzu nan tabar sak’e-sak’en zucin da take. “Fannah yanzu ya kenan? Sako ki Anas yayi bayan da gaskiya ya bayyana? Shi ya koreki? Bayan shi ya rabaki da budurcinki ya koro ki yanzu? Kuma kice kar in sanar da iyayensa abinda yayi? Wallahi a’a Fannah inke bakisan ciwon kanki ba ni nasani ina wayata.” Hannunta Fannah ta riqo “Mami calm down Anas bashi ya koreni ba hasali ma yanzu haka nasan kuka yake saboda yana cikin hakan nafito na barsa.” Komawa tayi ta zauna “ban fahimce kiba Fannah.” “Mami ni na k’are zamana da Anas yak’i bani takarda na shiyasa nadawo hakan.” Mamaki ne kwance a fuskar Mami. “Kinsan ban fahimce kiba har yanzu” abinda ta iya cewa kenan. Nan Fannah ta kwashe labarin komai tabata. “Haba Habibti! Taya zaki tafka sokanci haka? Kina ganin akwai d’a na mijin da ze rik’e ki da mutunci kaman yadda Anas zeyi ne? Wallahi babu. Tunda yayi nadama Fannah gakuma dalilin dayasa faruwan hakan ai seki yi hak’uri ki yafe masa nasan da zafi amman hak’uri zakiyi. Ni wallahi na d’au ma ko shi ya koroki dan shine babban tashin hankali, Anas na sonki so na hak’ik’a ba kowa neba ze iya yin abinda yayi ko baki tab’ajin inda za’a kama yaro nama d’iya fyad’e amman ya bushar da ido yace ba shine ba kuma ba yadda aka iya haka za’a barsa amman Anas fah? Ya yarda shi ya miki kuma ahakan kin still yakeson ki kiyi tunani Habibti.” Ta k’are maganar tare da riqo hannun Fannah cikin nata. Hawaye take sosai “Mami bawai yafiyan bane barin iya ba tsab zan yafe masa, ni nama yafe masa komu muna ma Allah laifi kuma ya yafe mana muddin mun tuba kamar yadda Anas yayi na yafe masa har abada kuma zan sanar dashi amman Mami barin iya zama dashi ba again, Mami abinda yamin da ciwo.” Kwantar da ita Mami takuma yi ajikinta. “Shhhh! na gane halin da kike ciki Habibti is not easy you need some space, da zafi sosai ace bada sanin kiba kin auri wanda ya miki tabargaza da rayuwa amman Habibti yariga ya wuce lets face the future ko ba haka ba?” Kai ta gyad’a a hankali. “Good kuma kema nasan kinason Anas ko bahaka ba?” Nanma kai ta gyad’a. “Toh alhamdulillah zaki cigaba da zama ana har nan da lokacin da kikejin zaki iya komawa d’akin ki shikuma Anas zan masa bayani.” Kai ta d’ago a raunane “Mami banason sake-” katseta Mami tayi da wuri ta hanyan aza yatsanta kan bakin ta tana kad’a mata kai. “Karkice haka Habibti karki kuskura kinji? Dole zaki koma gidan mijinki d’akinki tunda be sallameki ba kuma tambayan takarda haramun ne kema kinsani tsinuwa ake gaggautawa duk macen datayi hakan, ki hak’uri Fannah nasan yadda kikeji amman hak’uri yazama dole kinada nan da sati biyu ki huta hankalinki ya kwanta kafin Babanku ya dawo, kinsan muddin yaganki anan ze tambaya dalili, ko kinason yagano Anas ne yayi raping naki?” Da sauri ta kad’a kai. “Masha Allah kinga sekiyi hak’uri Anas nasonki Fannah godiya yakamata kiyi wa Allah ki tuna da irin walaqancin da Farouq da Ya Khaleel suke miki ada dakuma gori acewarsu ba d’a na mijin da ze tab’a aminta ya aureki karkiyi ma Anas haka Fannah, abinda ya miki ya riga ya wuce hak’uri zakiyi wannan shine jarabawarki a rayuwa kinji? Accept it Mamana.” Kai ta gyad’a a hankali badan tanaso ba. Mik’ewan Mami yayi daidai da shigowar Afrah d’akin a gurguje. “Ya haka?” Mami ta tambayeta. “Mami Ya Anas ne yazo” ta fad’a tana haqi “kuma.. Kuma.. Mami kuka yakeyi wallahi Ya Anas yazo yana kuka.” “Subhanallahi to kekuma me haka? Sekace kinyi gamo da aljan.” Kukan Fannah ne ya katse Mami daga magana. “Mami wai meke faruwa?” Cewar Afrah bayan ta kalli Fannah. “Babu kifita ina zuwa” badan tanaso ba tafice. “Fannah wai baraki bar kukan nan ba? Ko sena sa kinbi Anas kukoma tare?” Kai kawai ta girgiza mata “taso muje mu samesa.” “Mami banaso dan Allah kije ke kad’ai dan Allah.” Ba tare da ta saurareta ba taja hannunta tare da dank’a mata hijabinta “sa!” ta buk’aceta a tsawace. Da shegen tsoronta batasan lokacin da tasa suka fito ba hannunta na rik’e cikin na Mami. Zaune kan tabarman da Afrah ta shimfid’a masa suka tarar dashi ya had’a uwa uba tagumi kamar wanda yayi ciwon amai da gudawa ya zube arana d’aya tsantsan tashin hankali kawai, ko noticing su Mamin ma beyi ba tsabagen yadda ya zurfafa cikin tunani seda ya jiyo muryar Mami tana kashe wa Fannah warning hankalinsa ya dawo a garesa. “Ya isa haka!” tace. A raunane ya d’ago jajayen idanunsa ya azasu kansu Fannah. Zamansa ya daidaita ayayinda suka k’ariso kan taburman suka zauna a nitse, Fannah na a lab’e bayan Mami ko d’ago kai ta kallesa bataiba dukda jin idanunsa da take akanta. K’ok’arin dakatar da hawayen nasa yake amman ya kasa Afrah dake lab’e jikin k’ofa Mami ta umarceta da ta fice wajen gida kuma koda Aiman ta dawo karta barta tashigo se in sun gama maganan da zasuyi ba gardama ta fice. A sannu Mami ta dawo da kallonta kan Anas tana ganin yadda yake hawaye kamar ba gobe kallonta ta kewayo kan Fannah itama same story sede ma kamar Anas yafita yin kukan. Daga bisani Anas ya soma magana cikin sautin kuka cike da nadama. “Mami I’m sorry dan Allah kiyi hak’uri keda Fannah daduk wanin danayi hurting sanadin abinda na ma Fannah kuyi hak’uri dan Allah I’m truely sorry.” Sam yi tayi kamar batada labari saboda so take ta tabbatar da ko eh dagaske Anas yake ya tuba. “Wani abu kenan Anas? Meya faru? Kai kuka Fannah kuka ku fahimtar dani meke faruwa nayi nayi Fannah ta sanar dani amman taqi.” Alokaci d’aya Fannah ta d’ago kai tana kallon Mami fuska d’auke da tambaya amman kuma se tayi shiru. Idanunta na had’uwa da na Anas tayi saurin sadda kanta. “Mami kina nufin Fannah bata fad’a miki mena mata ba?” ya tambaya cikin dashasshiyar murya cike da rashin yarda da abinda Mami ta fad’a mai. Kamar ya Fannah bata sanar da ita abinda ya faru tsakaninsu ba??? “Eh Anas nide na ganta da akwati gakuma kukan datazo tana tayi shin meya faru? Sakinta kayi neh?” “Mami barin tab’a sakin Fannah ba har abada barin tab’a iya rubuta mata takardan saki ba, ina matuk’ar son Fannah fiye da yadda nakeson kaina...” Sekuma yayi shiru yana tunanin koya sanar da Mami abinda ya had’asa da Fannah ko a’a. But what if Mami tak’i yarda da tuban da yayi kamar yadda Fannah tayi kuma fah? What if ta tilasta sa seya saki Flowersa fah? No bare iya ba, he will never let that happen on the otherside kuma yanason yayi clearing komai tsakaninsu ko halan inyayi hakan Mami taji k’ansa tabarsa da matarsa. Tunanin wani ra’ayi d’aya zebi yake. Shirunsa yabawa Mami daman magana “Anas kayi shiru” dankuwa ta riga ta yanke hukuncin cewa inhar Anas bare iya confessing laifin daya aikata ba to be tuba dagaske kamar yadda Fannah ta fad’a mata ba inkuwa yayi toh Fannah is his! *ina fatan each and every fan tayi sallah lafiya, Allah maimaita mana Ameen, love you loads* [12:58, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 7⃣3⃣ Hannu yasa ya share hawayensa tare da jan numfashi sannan ya soma maganar a hankali cike da nadama. “Mami tabbas na tafka babban kuskure a rayuwa na, kuskuren da har a yau ina nadaman aikatasa but believe me when I say this wallahi nima ba’a son raina hakan ya faru ba. Kuma wallahi tun ranan da abin yafaru nakasa samun sukuni a rayuwa na akullum ina tunanin wani hali na jefa yarinyar if only I can reverse time da nayi dan daidaita komai. Mami shekaru bakwai da suka wuce ni nayi raping Fannah, nine nan silar duk wani abin takaici da bak’in cikin rayuwa da kukayi witnessing dan Allah kuyi hak’uri...” Kuka ne yafi qarfinsa yakasa k’arisa maganan duk anan Mami batace masa ko k’ala ba ido ta zuba masa ga wani uban tausayinsa dake shiganta, Fannah dake gefenta ba abinda take itama se kuka daga bisani ya cigaba “kuyi hak’uri dan Allah Mami wallahi inason Fannah karku rabani da ita, ni na raba ta da budurcinta kuma zan cigaba da zama da ita kar a rabani da ita dan Allah na tuba...” Ya k’are maganar cikin sautin kuka. “Naji bayanin ka Anas kuma na gamsu hak’ik’a ka tuba kuma kayi nadama tunda har ka iya ka yi confessing babban laifi irin wannan tabbas ka tafka babban kuskure amman tunda kayi nadama komai ya wuce yanzu sede abu d’aya da nakeson sanar dakai shine shi muslimi da tawakalli aka sansa, Fannah tamin bayanin komai na maka k’arya akan bata fad’a min ba saboda inason ji daga bakinka inkuma tabbatar da eh ka tuba dagaske kuma kayi. Hak’ik’anin gaskia ba na mijin da zeyi zaman mutunci da Fannah kamar yadda zakayi Anas hasali ma mune da godiya zanyi iya qoqari na dan ganin Fannah ta koma gidanka amman barin tilasta mata ba saboda abinda yafaru a tsakaninku da ciwo Anas she needs some space kuma ni na yafe maka duk mun yafe maka ina fatan Fannah ma zata yafe maka wannan abu yazame sirri a tsakaninmu ko Babansu barin sanar dashi ba zan barku tare” tana kai nan ta mik’e haka Fannah ma. Da sauri ta dakatar da ita “A’a Fannah ki zauna ku gana kikuma yafe masa kinji Habibiti?” Kai kawai take girgizawa tana hawaye “yi hak’uri ki zauna” nan ta shige d’aki. Itama Fannar hanyan d’akinsu ta kama bi dan ko batasan me zata fad’a mai ba, kamar a kyaftawan ido Anas ya mik’e ya riqo hijabinta “Fannah dan Allah karki tafi I’m sorry please forgive me.” Har a yanzu takasa furta koda ‘A’ a nitse ya juyo da ita suna fuskantar juna yunk’urin sauk’a kan guiwoyinsa ya gwada tasa hannu da sauri ta tarosa cikin sautin kuka tace “Anas dan Allah kabari dan Allah stop it na gamsu da tubar da kayi kuma na yafe maka zaka iya tafiya.” Hannunta daya gwada tab’awa taja da sauri tak’unsa cikin hijabinta. “Fannah thank you, thank you so much yanzu ne zan iya samun sukuni a rayuwa na, I can be free now amman dan Allah karki barni Fannah lets go home please I love you.” “Anas I can’t dan Allah kabarni katafi please” tana kaiwa nan ta fisge hijabinta ta shige d’akinsu. Kuka sosai ya tsaya yatayi awajen Mami ce tafito ta riga basa hak’uri takuma tabbatar masa cewa Fannah zata dawo a garesa saboda tana sonsa da k’yar ta iya tura Anas ya tafi koda yafito beyi takansu Afrah ba motarsa ya nufa ya wuce a 360 isarsa gida keda wuya ya had’a akwatin kayansa dawani duk abinda ze buk’ata ya rufo gidan ya wuce paint house nasa daga ranan ya soma rayuwa achan abinci ma ba ci yake ba se in yunwa ta gasa sa. Koda su Ummie suka mai waya za suzo dubansa da Fannah kuwa k’arya ya musu yace sunyi tafiya basu gari. A kullum cikin tunanin Fannah yake har kamar ya fara zarewa dan yana zaune shi kad’ansa seyaji wai Fannah na kiran sunansa cikin sarqarqiyar muryarta me bala’in masa dadi hotunanta ne suka zamo masa farillah dan a kullum pictures nata na a gabansa yana kalla. Akwai lokacin da damuwa suka ma Anas yawa kad’an ya rage ba’a koma gidan jiya ba tunda ya sanar da Mustea halin da yake ciki Mustea ya k’arfafa masa guiwa kan yanemi syrup kawai yasha amman dan promise daya d’aukar wa Fannah ya hana kansa da k’yar, bare iya explaining how much yayi missing Fannah ba duk yabi ya rame ya fita daga kamanninsa gabad’ai office ma yabar zuwa duk yamusu k’arya yace yayi tafiya. Morning, afternoon and night messages kam bebar sending ma Flowersa ba dukda ba replying nasa take ba. Ya kirata har ya gaji amman bata picking koda ya kira ta wayar Afrah dan a had’asu ma nan bata karb’a. A takaice de rayuwar wannan masoya biyu ya jagule cikin sati biyun da sukayu batare da sunsa juna a ido ba. Ba aikin Fannah a kullum se kuka, bata tab’a sanin tanason Anas ba seda ta dena ganinsa a ganga da ita da daddare kuwa kullum tazo bacci seta rungumo pillonta setanaji kamar Anas nata ne. Wayarta na maqale a hannunta a koda yaushe tana karanta lovely heart touching messages da Anas yake mata sending wanda take matuk’ar jin dad’insu amman batajin zata iya replying nasa back aduk lokacin da tunanin abinda ya faru tsakaninsu yayi crossing mind nata. Ba yadda Afrah batai da ita ta gaya mata meke faruwa ba amman tak’i ta d’au alk’warin riqe wa mijinta sirri. Abinci kam ba takansa take ba se sunyi fad’a da Mami take chi shid’inma kad’an take tab’awa. Akoi lokacin da su Mami sukayi Eghusi soup da pounded yam tana gani kawai ta tuna da Anas ta tuna da yadda yakeson miyan kawai ta b’arke musu da kuka. ***** “Fannah! Fannah!” Kiran Mami daga d’akinsu da Baba. Fannah dake d’akinsu miqe kan sallaya tana aikinta na kullum wato kuka tayi saurin share hawayen ta danko in Mami taganta zasuyi fad’a. “Na’am” ta amsa agigice tare da zabura ta nufa d’akinsu Baba chan ta samu Mami. “Bade kuka kike ba?” Cewar Mami kafin Fannah ta amsata ta cigaba, “karki damu na riga na ma Anas waya yau zezo ya d’aukeki kowa ma ya huta kinsan gobe Babanku ze dawo-” katseta Fannah tayi. “Mami dan Allah karkimin haka ko kwana biyu kibarni in k’ara anan.” “Nak’i Fannah ke wai bakida tausayi ne? Kinsan irin halin da kika jefa Anas tafiyarki kuwa? Yaron nan ya tuba mesa baraki yafe masa kukoma ku cigaba da zaman ku tare kamar yadda kuka saba ba? Ko wai acewarki akoi d’a namijin da ze kula dake ne kamar yadda Anas zeyi? Tun ina ganin abin naki da hankali na dena yanzu maza wuce ki shirya kayakin ki da La’asar Anas zezo ni na fad’a miki.” Har k’asa Fannah ta sauk’a tana had’a Mami da Allah amman ko a bakin zaninta ta fice tabar mata d’akin. Seda tayi me isarta sa’annan takoma d’akinsu takasa koda shirya kayakin nata zube take kan gado tana kukan da ita kanta batasan dalilinsa ba tana cikin haka taga call daga Anas bayan ya kwana biyu be kiranta se saqonnin dayake mata me zece mata yau? Ze zo ya d’auketa ko meh? Tana gani har yamata 2 missed calls tak’i picking bada jimawa ba ya turo mata message. _Flower please don’t be mad I’m sorry and I love you #kisses_ Wani sabon kukan ta fara seda tayi ta godewa Allah sannan ta tashi ta jawo akwatin ta sam takasa cika kayakinta ciki daidai nan da shigowar Mami kenan baki ta sake ganin akwatin Fannah empty batako soma shirya kayakin nata ba. “Yanzu Fannah baki ko fara shirya kayakin naki ba bayan kinsan La’asar ya kusa?” A marairaice ta d’ago idanunta tana kallom Mami. “Mami dan Allah kibari ko gobe se in tafi.” “Mschww! maganan banza” wardrobe nasu tanufa ta bude tare da ciro kayakin Fannah kap tasasu cikin akwatin tayi zipping se roqarta Fannah ke amman ko ta kanta Mami batai ba tsab ta had’a mata kayakinta masu dotti tasasu cikin leda ta had’esu gu d’aya. _4:12PM_ Shigowar Anas gidansu Fannah kenan Mami kanta data gansa seda ta tsorata tana cewa Fannah ta rame ta lalace amman farillah ramanta yake aganga dana Anas sam kamar ba shiba bayan gaisuwa Mami ta sake basa hak’uri sosai sannan kuma ta masa nasiha daga nan tashiga dan fito da Fannah drama sosai suka riqayi sannan da qaqani qaqa tasamu ta fito da ita, akwatin ta Anas ya amsa. Wa’azi me ratsa jiki Mami ta musu sosai duk jikinsu ya sake mutuwa barin ma Fannah, da k’yar tafito daga gidan iya bakin k’ofa Mami ta musu rakiya ta koma ciki. “Fannah please lets go kinji? Kiyi hak’uri kibar kukan nan please lets go.” Sam tayi kamar bada ita yake ba sun kusan minti biyar tsaye wajen ganin batada niyyan ko motsawa ya finciko hannunta. “Anas ka sakeni ka sakeni nace” da dambe ya k’arisa motan da ita ya bude’e mata gidan gaba yasata sannan ya sanya jakarta a baya yazagayo shima ya shiga. Tunda suka fara tafiya take masa kuka a mota koda suka isa gida kuwa tafito bata ce masa komai ba akwatinta taciro ya karb’e mata. Shigarta ciki ta nufa d’akinta ta baje kan gado, bayanta yabi yakai mata akwatinta. “Flower kinci abincin rana?” Ya tambayeta baya ta juya masa. Nufowa gabanta yayi nanma ta sake juyawa “Flower meh kikeson ci? Yi hak’uri ki fad’a min” nanma banza dashi tayi haka yata suratansa har yagaji bata tanka sa ba seda ya fita ta mik’e tashiga bayi ta watsa ruwa fitowarta yayi daidai da shigowar Anas da plate na kaza a hannunsa. A farko tayi niyyan komawa cikin bathroom d’in dankuwa gajeren towel ne ajikinta daga baya data tsaya tayi tunani cikin d’an k’ank’anin lokaci kuwa setaga yin hakan bayida amfani tunda ya tab’a ganinta ba kaya ma a jikinta. Ignoring nasa tayi ta nufa wajen dressing mirror har anan bebar kallonta ba he can’t explain how much he missed her body. Daga bisani ya girgiza kai “Fannah I’m sorry bansan...” Sekuma yayi shiru yaja k’ofar ze rufe kenan ta ce dashi “ba komai.” ba tare da ta kallesa ba. Sam be yarda da abinda kunnuwansa suka jiye masa ba be d’au Fannah zata sake masa magana bama, lallai inta haka he has a chance. A nitse ya k’ariso cikin d’akin “gashi incase you are hungry eat please” ya ajiye mata plate d’in kan dressing mirror. Seda ya kai da bakin k’ofa sannan tace masa “nagode.” Dad’i sosai yaji “you are welcome Flower.” Yana kaiwa nan ya fice yakoma parlour ya zauna yana jirar ko zata fito. Bada dad’ewa ba k’ofarsu yayi k’ara yana dubawa yaga sabin fuska guda biyu da alama ma mata da miji ne wani button ya danna se main gate ya bud’u nan ya fito dan tarerayarsu. Bayan ya shigo dasu sika gaggaisa. “So gidanmu ne kusa da naku by the left lokacin da kuka zo nan munyi tafiya nida HASKE NA dawowan mu kuma mukaji wai kuma kunyi tafiya d’azu Haskena kecemin ta ga shigowarku shine nace mata yakamata mushigo mu muku sannu dazuwa.” Cewar mijin. “Suna na MUS'AB wannan kuma is my wife NAINAH” yajuyo ya sakar mata dawata lallausassar murmushi, murmushin ta miyar masa itama. Haka kawai se Anas yaji sun burgesa se ya tuna lokacin da suke a haka shima shi da Flowersa he misses her alot, da k’yar ya iya bud’a baki yayi magana drinks yayi serving nasu ganin Fannah batada niyyan fitowa ya shiga mata managa mik’e kan gado ya tarar da ita. Bayan ya k’arisa ya zauna agefenta yace, “Flower munyi bak’i neighbours namu ne suka shigo mana inda zaki iya fitowa seku gaisa da matarsa.” Kai ta gyad’a masa. Daman da hijabi jikinta bayansa tabi suka fito daya gwada yunk’urin riqe mata hannu kuwa setaja da baya. “Flower just for this once se mun nuna musu we are not on good terms ne? Please corperate” Sam tak’i barinsa ya tab’a mata hannu haka ba yadda ya iya suka fito kai a rabe idanunta basu sauk’a ako inaba se hannun Mus’ab da Nainah data gani a had’e se hirarsu suke suna dariya gwanin sha’awa a hankali ta dawo da kallonta kan Anas ita kanta she miss yadda suke a da. Ahakan suka k’ariso parlour’n suka zauna a seperate kujera tun anan hankalin Mus’ab yabasa da akwai matsala bayan sun gaggaisa cike da dabara ya buk’aci Fannah dasu shiga ciki da Nainah, hakan kuwa akayi. Alokaci guda Fannah taji san Nainah yashigeta ganin yadda take small of age amman ga hankali da ladabi da biyayya sede ashe ba Mus’ab ne kad’ai yagano abinda ke faruwa tsakanin Anas da Fannar ba har ita Nainan ma tayi. Suna zaune kan gado bayan Nainah tagama yabawa d’akin Fannah dama gidan entirely tayi gyaran murya. “Aunty Fannah” tace da ita. “Na’am Nainah” ta amsata. “Ba shisshigi ba Aunty amman senaga kamar da akoi matsala tsakaninki da Uncle.” Bata bar Fannah tayi magana ba ta cigaba “shi zaman aure se hak’uri Aunty koni da kike gani na nan inada kishiya kuma bawai shiri muke da ita ba sau dayawa tana cewa seta kasheni hakan be bani daman fad’a da miji na ba ina sonsa kuma shima yana sona kamar yadda nasan kuma kuna son junanku.” Wa’azi sosai Nainah ‘yar shekaru sha bakwai ta tama Fannah liqis ta kashe mata jiki gakuma wani kunyan dataji ache k’anwar bayanta tamata gyara bisa ganganci irin nata dan ko bata tambaya ba tasan Afrah ta girmi Nainah. Godiya sosai Fannah ta mata tare da bata kyautan wasu bangles had’ad’d’u. Shima Anas tun zamansa da Mus’ab ya riga masa wa’azi da nasiha sosai. **** Bayan sun yi masu rakiya suka dawo ciki har Fannah takai da bakin k’ofar d’akinta sekuma ta tuna alk’awarin data ma Nainah nacewa zata bawa Anas hak’uri bisa hurting nasa datayi. Seta juya zata masa magana sekuma ta kas, shiko yana tsaye a tsakar parlon ya k’ura mata ido ji yake kamar yaje yayi hugging nata ya fad’a mata how much he loves her. Da k’yar ta iya kiran sunansa muryarta se rawa take. “Anas” daman jira yake ya amsa “na’am Flower” tare da takowa har gabanta dududu space daya rage a tsakaninsu befi inches shida ba. Kanta ta sunkuyar “Anas I’m sorry kayi hak’uri” ta fad’a dashi sincerely. Hannunta duka ya rik’o cikin nasa d’aya yana murzawa a hankali tare da mata wani erin kallo alokaci guda yaji bak’in cikinsa duk sun gushe, murmushi ne fal kwance a kan fuskarsa. Dad’i yaji sosai da bata hanasa rik’e mata hannu ba. *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:58, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 7⃣4⃣ D’ayan hannunsa ya aza a hab’arta tare da d’ago fuskartata. “Flower you don’t have to be sorry baki min komai ba, ni ya kamata in baki hak’uri and not the other way round I’m sorry kinji?” Kai ta gyad’a ba tare da tabari sun had’a ido ba. “Flower baraki kalleni ba?” ta kad’a masa kai. “Then look at me” ba musu ta miyar da kallonta kan kyakkyawar fuskarsa, murmushi ya saki mata yana kallon cikin idanunta. “I miss your body can I hug you?” Hannun ta taraba daga nasa tare da gyad’a masa kai nan ta rungumeshi shima haka, hugging juna passionately “I miss you too Anas.” Sun d’au tsawon lokaci suna manne da juna suna jin dad’in k’amshin jikin junansu sannan daga bisani tayi breaking hug d’in tare da juyawa zata shiga d’akinta, hannunta ya riqo da wuri “Flower muje muci abinci kinji?” Kai ta girgiza masa nufin bazata ba. “Flower bakiya jin yunwa?” Ta gyad’a kai “please muje nasan kinaji lets go.” “Barin jeba” ta fad’a tare da shigewa d’akinta. Badan yanaso ba yajuya ya shiga d’akinsa ya canza shiri bayan ya fito ya rufo k’ofar juyawansa kawai ya tarar da Fannah tsaye gefen motarsa idanunsa ya sosa da kyau dan tabbatar da abinda yake gani. Murmushi ta saki masa “yi sauri ka bud’e min rana.” Kasa danna security d’inma yayi duk ya kid’ime sosai navy blue hijabin dake sanye jikinta ya mata kyau seda ya gama k’arisowa gabanta ya tab’a hannunta dan tabbatar da ko eh dagaske itan ce sannan ya bud’e motar mata da kansa, bayan tashiga ya rufe sannan ya zagaya shima ya shiga suka fice. Hira d’ad’d’aya yake mata wanda ba duka take amsa shiba har suka isa inda zasu. Daidai gaban DERIBE HOTEL suka tsaya dan chan yayi reserving bayan ya bud’e mata k’ofa ya rik’o hannunta, shigansu ciki taga yayi reserving as always. Cikin wani irin salon da bare basa haushi ba tace, “Anas baka iya chin abinci se kayi reserving?” Kai ya gyad’a mata “why?” Ta tambayesa “saboda banason hayaniya.” ya amsata. “Kasan meh?” “A’a meneh Flower?” “Inason yau muje inda bakayi reserving ba muci abinci inason ka koyi cin abinci in public its fun.” Sam beji dad’in wannan shawara na Fannah ba haka yake bai iya cin abinci in public ba, ko days back dayake boarding school sede ya taho da abincinsa hostel yaci inkuma aka hanasa, abincin da bayya chi kenan. “Anas Habeebi” ta kira sunansa ganin baida niyyan magana. “Bakaso?” “Inaso Habibti lets go” ya mata k’arya nan suka juya GRAND PINNACLE HOTEL LUXURY suka dosa bayan sunyi placing order bada jimawa ba abincin nasu ya iso tun anan yanayin Anas ya canza daya juya yaga mutane anan mutane achan ga wasu yara masu uban surutu se distracting nasa suke abinda ya wasa kenan. Har takai spoons biyar Anas be tab’a nasa ba. “Anas mesa baka chi?” “Flower the truth is am not used to it ban iya chin abinci cikin mutane ba.” Qasaitacciyar murmushi ta sakar masa tare da matso wa kujeran dake kusa da nasa ta zauna spoon d’aya ta d’aga ta kai masa baki. Kallonta yake kawai cike da adoration wani sabon santa na sake shigansa. “Ahhh” ta buk’ace sa. Murmushi ya mata sannan ya bud’e bakin nasa ta basa, haka ta riga basa seda yace ya k’oshi anan ne itama ta jawo na ta plate zata cigaba daci amsar plate d’in yayi “my turn my lady.” “No nikam zanci da kaina.” “No Flower let me kinji?” Kai ta gyad’a masa haka yariga bata itama seda tayi nak! “Look around you” ta buk’ace sa bayan ya juya ya k’are wa mutanen cikin kallo sosai yaga lessons kowa da kalan rayuwarsa ga masu jiran mutane su gama cin abinci su d’au nasu suma su samu su chi, da wanda suke sharing abincin plate d’aya mutane de daban-daban. “Kaga yawan shiga cikin jama’a nasa mu sake godewa Allah cikin yanayin da muka tsinci kanmu for instance kalli wanda suke tsaye bakin k’ofa achan ko kud’in abincin ma basuda kaga anan se ka sake godewa Allah right?” “Right Flower” ya amsata cike da jin dad’i “Alhamdulillah!” nan ya biya musu kud’insu da suka fito kuwa irin mutanen wajen nan duk yabisu ya rarraba musu kud’i dad’i sosai Fannah taji tun daga ranan Anas ya koyi chin abinchi cikin jama’a although atimes seyayi reserving waje still. Koda suka dawo gida shi ya taimaka mata ta had’a kayakinta cikin wardrobe nata bayan nan suka miqe kan gado suna hira abinsu gwanin sha’awa Fannah na viewing pictures nata da Anas yakeda su cikin wayansa wanda kap batasan lokacin daya d’aukesu ba tana cikin haka Angel ta soma kira nan ta miqa wa Anas. Bayan sun gaisa Amal tasoma k’orafi. “Shikenan Ya Anas tunda kayi aure kadena sona nasani yanzu se Ya Fannah kakeso.” Dariya sosai shida Fannah sukayi “inji wa Angel? I love you both, no one like you kinji? Kibar had’a kanki da Fannah.” Amsar wayar Fannah tayi. “Amal karki ce haka kinga nima yanzu mukayi fad’a da Anas cemin yayi yafi sonki akaina.” “Kai Ya Fannah bawanin nan.” “Dagaske Angel na Ya Anas.” Dad’i sosai taji toh shikenan ba-bye tayi hanging. “Toh Mr. Fauzi kaji Amal tana k’orafi gobe yakamata ka mata shopping ka kaimata.” “Angama Mrs. Fauzi your wish is my command.” Oh hakane yanzu? Ko ka manta kaine Boss d’ina? “Ada kenan Flower but now kece Boss... Me kikeyi?” ya tambaya ganin ta seta cameran wayarta kansa. “Abinda ka saba min, now I have 5 of your pictures” “LOL kin rama kenan? Let me see them” “Fad’i gaskia de so kake ka goge barin bada ba” tana kaiwa nan ta miqe da sauri ya jawota ta fad’a jikinsa k’ok’arin k’wace wayar yake ta duk’un’kunesa cikin hannunta tasa a kayanta acewarta ahakan bare iya amsa ba. Murmushi yasaki sannan yasa hannu cikin kayan nata ya zaro wayar sanadin haka yasata dariya se kamar chakulkuli yake mata. Fuska ta maraice “karka goge please kaji Habeebi.” “Tell me you love me.” “In nafad’a baraka koge ba?” “Yes Baby” ya gyad’a mata kai. “Okay Mr. Fauzi I love you I love you so much” tayi pecking nasa a kumatu. “Bani toh.” ***** _5:20AM_ Bayan sun idar da Sallah suka koma suka kwanta kamar yadda suka saba a kullum. Hannunsu ya had’a “Flower yau bakiyi mafarki ba” “Yes I’ve found you already ai bawani mafarki kuma.” “I’m sorry kinji Flower for hunting you like that.” “Nima I’m sorry lets sleep kasan akoi office yau.” “Ni barinje ba.” “Lallai kuwa Mr. Fauzi kafara wasa da aiki.” “I don’t want to leave you Flower.” *_“INA TARE DA KAI_* My Lion am never leaving you.” Dad’i sosai yaji yayi pecking cikin gashinta. “Aha! I have a suprise for you yau around 1:30PM zanzo in d’aukeki kinji?” “Naji meh suprise d’in?” “Ai ba’a fad’an suprises Flower just keep calm.” Ahaka suka koma bacci. _7:40AM_ “No goodluck kiss Flower?” Cewar Anas suna tsaye bakin k’ofa hannunsa rik’e da nata d’ayan kuma lunch nasa. Murmushi ta saki masa “babu sakemin hannu inkoma ciki take care of yourself for me, I love you.” “You must kiss me first.” Kafad’a ta buga masa “seka dawo.” “No ni yanzu nakeso” “Then ka fad’a min meh suprise d’in ko hint ne kabani kaji Habeebi then I will kiss you” ta k’arisa maganan hannunta biyu zagaye a wuyansa. “Flower suprise ne I can’t tell you.” “Shikenan nima I can’t kiss you” hannayenta ta cire daga wuyansa, da sauri ya zagaye nasa hannun a ‘yar kunkuminta “you must Flower.” murmushi ta masa sannan tayi d’agel tayi grabbing lips nasa batasan a lokacin da ta kai hannayenta cikin gashin kansa da yayi styling ba d’azu kap ta hargitsa masa dan yadda kissing nasa ke tafiyar mata da imani se chan da tayi pulling out ta masa murmushi, shima murmushin ya mata. Idanunta na sauk’a kan gashinsa ta waro idanu. “Ya Salam Habeebi kaga gashinka its all a mess!” “Toh ai kece, ke kika hargitsa min.” “Toh ai kaine I lose control whenever I’m kis-” sekuma tayi shiru takasa k’arisa maganan dan wani kunyan dataji ya ratsa ta ita kanta batasan ya akayi ta fad’i wannan maganganu ba. Kai ta sunkuyar a yayinda yasa hannu a k’ark’ashin hab’arta ya d’ago fuskarta, fuskarsa d’auke dawani shu’umin murmushi. “Flower me kikace?” Kamar wacce baratayi mgana ba kuma setace “babu zakayi latti katafi kaji?” “Se kin d’ago idanun ki kin kalleni ki kuma nanata min abinda kika fara fad’i dazu zan tafi.” Sun d’au minti uku suna tsaye ahaka ganin baida niyyan tafiya tasa ta d’ago idanunta ta azasu kansa. Hannu ta d’aga ta soma gyara masa gashin kansan duk anan yana binta da kallo seda ta gama sannan ta maido da kallonta garesa. “Habeebi I lose control whenever I’m kissing you.” “Mesa?” ya tambayeta “Because...” ta aza yatsanta kan lips nasa “they are sweeter than honey.” Sam seji yake kamar a mafarki anya kuwa wannan ce Fannar daya sani me uban kunya? “And yours too Baby.” Murmushi tamasa “off you go nima I have a suprise for you se in ka dawo.” I love you sukayi exchanging sannan ya fice farin ciki fal kwance a fuskarsa. By 12:30PM Fannah tagama had’a girkinta wanka tashiga da wuri-wuri tayi ta fito ta shirya cikin wani A shaped doguwar riga na lace, light makeup tayi applying ta kama gashinta gu d’aya sannan ta sanya hijabinta violet akai. K’arfe d’aya nayi ta idar da sallah tasoma zaman jirar Anas yau tunda ya tafi office be kirata ba ko aiki ne ya masa yawa oho. 1:40PM Anas ya dawo gida d’aukanta, kasa ignoring kyan da tayi yayi daya sata a ido seda ya sata gaba ya riga d’aukanta pictures, sam yak’i sanar da ita ina ze kaita sede daga baya taga sun fara dosan Enterprise nasa. “Habeebi meh zamuyi a Enterprise naka kuma?” “Kede tsaya ki gani mana Flower” kafin su kai da Enterprise d’in ya tsaya tare da ciro wani d’an bak’in k’yalle. “Turn around” ya buk’ace ta. “Meh zaka min da wannan kuma?” “Just trust me Flower.” Ba gardama ta juya ya d’aure mata ido sakwa-sakwa yadda bare dameta ba. Bayan sun k’arisa ciki yayi parking sannan yafito da ita a hankali daidai gaban Enterprise d’in ya tsaya da ita. “Are you ready?” Ya tambayeta. Kai kawai ta gyad’a. “Okay” anan ya kunce k’yallen. Kallonsa take a yayinda ya mata nuni da idanunsa akan ta kalli sama hakan tayi. Mamaki ne sosai ya cikata ganin sunan Enterprise d’in Anas ya canza daga FLAMES Enterprises zuwa FAHNAS Enterprises. “Woowww!” Ne kad’ai abinda bakinta yake iya furtawa har ayanzu takasa believing. “Habeebi this is amazing yayi kyau sosai, OMG! FAHNAS... me ma’anarsa?” “FAH-FANNAH NAS-ANAS.” “Awwwn! This is so romantic yayi kyau Allah k’ara bud’i ya karemin kai Baby I love you.” Hannunsa ya zagaye a kunkuminta daga gefe “I love you too Flower.” peck ta manna masa a kumatu. “Yaayi kyau sosai and I love it, much appreciated” wayarta ta ciro ta d’au gaban Enterprise d’in hoto. “So zamu koma gida kokuma zaka zauna anan se 4 kadawo gida?” “Kinason in biyoki mukoma gida yanzu?” “Ofcourse yes Habeebi.” “Toh muje Mrs. Fauzi” dad’i sosai taji bayan isowarsu gida duk suka rage kayakin jikinsu. “Ina suprise nawa Flower?” “Yana nan a dining table muje muchi abinci.” Hannunsa ta riqo bayan sun k’arisa dining ta bud’e d’aya daga cikin manyan flasks d’in tuk’ek’k’en tuwon semovita ne had’ad’e ciki nan tayi serving nasu duka shide Anas ya zuba mata ido tana bud’e flask na miyan ya toshe hanci tare da miqa wuya dan tabbatar da abinda zuciyarsa ke saqa masa. “Flower what is this?” “Meh kuwa ? Abinci mana Babe.” “Da gangan kikayi hakan koh? Eww! Close it please kinfa san banason wannan miyan kukan.” Nan ya miqe da wuri ta sake zaunar dashi. “Wai me haka Habeebi? Se wani toshe hanci kake sekace something is smelling.” “This is smelling Flower” ya nuna flask d’in “dan Allah ki rufe.” D’ago flask d’in tayi ta matso dashi gabansa tare da sauk’e hannunsa daya toshe hancin sa dashi daga fuskar nasa. “Flower stop it please” sewani yamutsa fuska yake. “Wannan ne suprise d’in? Na gani thanks sosai zanje in dafa noodules yau kowa yayi dining shi kad’asa kuma kisani nima se na rama ewww!” Ya watsa wa miyan kukan kallo. Kafin ya miqe ta dakatar dashi ta hanyan zama kan cinyarsa. “Flower yau neman tsokana na kike ko? Tashi please warin ya isheni.” “Haba Babyn Fannah, my Habeebi, my lion, my life and happiness” ta zagaye hannayenta a wuyansa cikin wani erin salon dake sosa masa zuciya. “Wani wari kuma miyan yakeyi? Trust me Allah ka tab’a kaji da akwai dad’i.” “Flower baya min dad’i please ki rufe.” “Yi hak’uri Baby ka tab’a kaji?” Kai ya girgiza mata “I will kiss you over and over and over yau kaji?” Nanma kai ya kad’a. Haka itama tak’i tashi masa daga cinya miyan ta zuba kan d’ayan plate d’in ta wanke hannunta sannan ta gutsira kad’an daga tuwon ta had’a da miya takawo masa baki. Hannu yasa da wuri ya toshe hancinsa “Flower please kibari” d’ayan hannunsa yasa ya shure hannunta baya aiko ta maidoshi gabansa. “Open up mana Baby.” Kai kawai ya kad’a mata, dabara ce ta fad’o mata. “Okay toh naji baraka chiba zan dafa maka noodules” nan ta miyar da plate d’in ta ajiye kan dining. “Toh ta-” bata bari ya k’are maganan ba ta cusa masa tuwon a baki nan danan ya fara yunk’urin cirowa “uhm-uhm Habeebi” ta kad’a masa kai tare da toshe masa hanci. “Had’e kaji Babe in bahaka ba barin sake maka hancin ba, sekace baturen gaske kace bakacin miyan kuka! Oya had’iye” da k’arfin da Allah ya bata ta matse hancin nasa ko kasa koda k’watan kansa ya yi. Idanunsa sun kad’a sunyi ja dan rashin numfashi sam yak’i had’iwa ganin ba mahalicci se Allah ya rufe ido ya had’iye badan yanaso ba. Se anan ta sake mai hancin tare da miqa masa ruwa tas ya kwankwad’e “tashi min Flower” ya buk’ace ta yana k’ok’arin k’irk’iro amai. “Ina zakaje?” Ta tambayesa. “I need to throw up kitashi please.” “Ai ina nan Anas yau seka koyi cin miyan kukan nan ina zanzo in kaika? Bakacin cous-cous, d’an wake, kuka, kub’ewa komai ma bakaci se abincin turawa? Gomma ka kwantar da hankalinka dan yau sekaci tuwon nan.” “Naji zanci tashi toh.” “Saboda kasamu chance na guduwa ba? Ba inda zani” nan ta d’au plate d’in ta sake had’a tuwon da miyar “oya open up.” Se toshe hanci yake har a yanzu yak’i bud’e bakin “Flower wai d’anki ne ni? Kibari in kika haihu sekiyi ma d’anki wannan forcing d’in ni baran ci ba.” “Naji amman kafin in samu d’an da zan masa zan fara akan Daddynsa oya open up.” “Naqi.” “Aw in sake toshe maka hancin kenan koh?” “Flower manaaa.” ya maraice fuska. “Yi hak’uri ka bud’e Baby na...” seda ta kusan kuka sannan Anas ya yarda ya bud’e bakinsa ta basa bayan ta basa kusan sau biyar sekuma yaji kukan ya masa dad’i compared to wanda ake musu a boarding house lokacin wanda sanadin rashin dad’insa yabar cin kuka kwata kwata. *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:58, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 7⃣5⃣ Sede still bayason miyan kukan yafison ire-iren abincin daya saba ci a London su burger, pizza, bufallo wing, glorified rice, louisiana da sauransu. Datazo sake basa hannunta ya rik’e “na k’oshi a banza bakin mutum ya fara warin kukan nan” “Ai sekayi brushing bale ma bawani warin nan, open up” “Na k’oshi” “Dameh?” Ta tambayesa. “Wannan” ya nuna mata da yatsa. “Haba Habeebi guda biyar fa kacal kachi yi hak’uri ka k’ara nasan kana jin yunwa yi hak’uri Baby” haka tariga lalashinsa kamar d’an yaro tana basa abincin da wayo cikin k’issa kafin su hankara har yagama plate nasa bakinsa ta wanke masa da kyau se anan ta tashi mai daga chinya dan chin nata itama. Tana tashi shima ya mik’e zasa toilet ya k’wak’ulo amai. *“Mine* ina zakaje? Bade toilet ba! Please karka je ka harar da abincin nan.” “Ohh! Flower ni barin iya zama da wannan kukan acikina ba.” “Nasani hak’uri zakayi Habeebi na zauna a parlour kajirani I want us to play a game today.” “Wani game?” “Just wait for me.” “Toh naji excuse me” nan ya juya. “Baby promise baraka je ka harar ba.” Shiru yayi yana nazari. “Baby please.” “Okay okay I promise shikenan?” Nan ta gyad’a kai bayi ya nufa yayi brushing shi wai a dole miyan kuka nasa bad breath (warin baki) dawowansa ya zauna kan d’aya daga cikin sofas na parlour’n tare da kunna cinema. Kasa kallon news d’inma yayi se kallon Fannah yake yadda take chin tuwon sekace wani abun arziki me dad’i. Da idanunsu ya had’u ya wani yamutsa fuska “zaka k’ara neh?” Da sauri ya kad’a kai “a’a banaso thank you.” Murmushi ta saki “karka damu gobe dashi zamuyi breakfast zanyi mana d’umamensa.” Blue eyes nasa ya k’wararo “zaki d’uma meneh?” “D’uma wannan ko bakasan meh d’umameh ba? Zan sake reheating tuwon mana muyi breakfast dashi.” “Keda wa?” Ya sake tambaya “Nida Habeebi na.” Kai ya gyad’a “lallai kam zaki nemi new Habeebi dan ni barinci d’umamen wannan abin ba.” “LOL” tad’an murmusa “ai kai ne kad’ai Habeebin nawa, trust me d’umamen ma yafi dad’i yafi taste kasan da me yau zamuyi dinner?” “A’a bansani ba and banason sani ki rik’e please ni kawai zansha coffee in kwanta barin chi komai ba.” “Kai Habeebi d’an wake de zan mana inyi slicing egg and cabbage akai its way yummy. Gode kuma in Allah ta kaimu miyan kub’ewa zanyi” Yamutsa fuska yayi “a’a Flower please kiyi abinki ke kad’ai naji yunwa ko sausages zan soya inchi.” “Oho nide d’an wake zamuci da Baby na.” Be sake ce mata komai ba har tagama chi ta tattara dining d’in sannan ta dawo ta samesa da paper dakuma biro biyu a hannunta, gefensa ta zauna. “X and O zamuyi.” Yana jin haka ya kad’a mata kai dan ko sam be iya game d’inba bayason kuma yayi losing a gabanta ta raina sa kokuma ya fad’a mata be iya ba ta masa dariya. “Baby kayi shiru.” “Barinyi ba ki kawo wani game daban wannan ba dad’i.” “Toh Habeebi ni shi kad’ai nasani Allah da dad’i lets try kaga.” “Ohh!” dabara ta fad’o masa “ni se yanzu ma na tuna inada aikin da yakamata inyi attending to a laptop” ya k’arisa maganan yana k’ok’arin miqewa hannunsa ta riqe ta dakatar dashi “Habeebi I can tell you are lying kode kana tsoron kar inyi winning naka ne” tamasa gwalo. “Ke kiyi winning d’ina? Impossible lets play it muga.” Nan da nan ta zazzana musu sannan ta mik’a masa pen d’aya zuciyan Mr. Fauzi fa se bugu yake dan sam be iya game d’in ba at all. “So deal d’in shine if I win zan d’aneka anan” ta nuna goshinsa. Shiru yayi yana nazarin yau d’ani nawa zesha gun Flower. “Baby kayi shiru ko kanajin tsoro ne? Karka damu I’ll take it easy on you” tana masa wani shu’umin murmushi. Ina irin shikuma bari ya nuna mata shina miji ne bayajin tsoron nan. “Ba tausayi in na nad’e ki se goshin naki yayi ja.” “Haka kace?” “Yes Flower haka nace.” “Fine lets start.” Shi yafara placing X bayan yayi itama tasa O kafin ya hankara Fannah ta masa baki biyu kafin yace meh tariga tayi crossing ta chi sa. Tsalle ta daka “yeyy! I won nachi!” “Taya ya kikaci? Ai wannan cuwa-cuwa ne niban yarda ba.” “Kamar ya Baby? Gashi nan nacika kuma kana gani bring your forehead.” “Gaskia ban yarda ba asake wani kinyi magud’i anan.” “No vex asake wanin.” Hankali sosai ya miyar yana coffan yadda tayi d’azu shima dan mata baki biyu sede nan ma kafin ya hankara tasake chi nanma tata daka tsalle “yes!! yanzu ka yarda na cika?” “Ni fa gaskiya ban yarda ba kina min cuwa-cuwa ne kawai.” “Koma me ka kawo goshinka saboda deal ne.” Fuskarsa ya ajiye mata daidai tsakiyan goshin sa tasa hannu ta danna masa d’ani me uban zafi take wajen yayi pink. K’ara ya saki “argghhh!” “Aww” tayi pouting bakinta “da zafi ne Baby?” “Nima bansani ba” ya watsa mata kallo. Zuciya yayi “lets play again I must win this time.” Nanma da suka buga ita ta sake chi haka ba yadda ya iya ta ya sake a jiye mata goshinsa ta d’anesa fiye dana d’azu nanma k’ara ya saki sosai amman kamar maye yak’i hak’ura shi a dole seyaci ta aiko sun buga har sau 7 duk Fannah kechi gashi ko saurara masa batayi tunda yace no pity haka take d’aninsa da zafi-zafi goshin Anas daga fari yakoma pink yanzu jazir ya koma duk yabi ya galabaita. “Mschww! Ni na fasa game d’in.” a fusace ya mik’e yashiga d’akinsa. Murmushi kad’an tasaki sekuma ya bata tausayi ga dukkan alamu be iya game d’in bane daman shegen ajeboncin sannan dama ina ze iya? K’aramar hand towel da warm water tasa a bowl tabi bayansa mik’e kan gado ta tarar dashi yana ganinta ya juya mata baya a nitse ta k’ariso ta ajiye bowl d’in akan side drawer sannan ta zaro robe daga ciki ta ajiye a gefe. “My Baby” ta kira sunansa. Ko juyawa ya kalleta ma beyi ba. “Habeebi yi hak’uri ka juyo kaji inga goshin naka.” Nanma shiru ya mata. “Yi hak’uri mana Baby.” “Me zaku gani? So kike ki gani kimin dariya komeh?” “Ko kad’an Habeebi taya zan maka dariya? Gani zanyi kaji yi hak’uri kajuyo.” Ganin baida niyan juyawa tasa hannu ta juyo dashi a hankali tare da aza kansa kan cinyoyinta ita kanta seda ta tsorata ganin abinda ta mai da goshi, wani erin fata ne dashi sekace na mace da baison wahala haka? “Ya Salam Baby I’m sorry bansan haka goshin naka yayi ba.” hannunta ta miqa ta tab’a goshin nasa k’ara ya saki sosai. “I’m sorry kaji? Kai kace fa no sympathy ba tausayi shiyasa.” “Toh kuma seki yarda? Aikinsan in nine barin miki haka ba.” yayi maganar kamar wanda zeyi kuka. “Baby I’m sorry da ka fad’a min baka iya ba ai.” “Flower its embarrassing ace ban iya playing simple game kaman wannan O and X d’inba.” “Baby its X and O ba O and X ba.” “Naji whatever” kansa ya d’ago daga cinyar nata ze juya mata baya kenan ta rik’o hannunsa. ”Don’t be mad kaji Habeebi? Game ne kawai ba komai ba I’m sorry kuma bar kan naka kan cinya na zan d’an matsa maka wajen ne” “Kin manta kwanaki da cintoyin sukayi tsami ne?” “Ina sane ai ba dad’ewa zakayi akai ba tsaya” Batare da yace da ita komai ba ta matse towel d’in ta aza kan goshinsa da wuri yasa hannu ze d’aga dan azaba ta dakatar dashi “sorry kaji? Nasan da zafi hak’uri zakayi” haka tata matse masa a hankali yana sakin k’ananun k’ara time to time bayan data tabbata ta matse masa ta bud’e robe d’in ta lak’uta tasa a goshin nasa tana fara murzawa yayi saurin d’aga hannunta. “Flower ya isa haka barshi.” “Habeebi ka tsaya ko kad’an ne in mirza in bahaka ba ze iya kumbura fah” “Toh ai laifin ki ne, ke kika riga d’ani na sekace ba mijin kiba” “Baby nace I’m sorry be wuce ba? yanzu tsaya mu shafa maka semu kwanta mu huta... Yawwa Baby naa” a hankali take shafa masa har tasamu ta gama taje ta zubar da ruwan sannan ta dawo suka d’aura alwala tare da yin Sallah. Gado suka haye suka kwanta tana a gefensa suna fuskantan juna. “I love you Anas.” Shiru ya mata shi a dole har yanzu yanajin haushi. “Baby baraka cemin I love you too ba?” Kai ya gyad’a. “Har yanzu wai baka hak’ura ba?” Nan ma kai ya gyad’a. Matsowa tayi gab dashi kafin ya gane me takeson yi kawai ta hau kissing nasa ganin basuda niyyan tsayawa nima naja legediz benz d’ina na bar musu d’akin gudun kar su cinye kansu a idanu na (LOL) Koda na leqosu bayan minti uku still basu bari ba haka na sake komawa nabasu minti goma anan ne dana leqo naga Fannah kwance kan k’irjin Anas murmushi fal kwance kan fiskokinsu yana shafa doguwar sumanta a hankali cike da soyayya. “So can I hear it now?” Ta tambayesa. “Yes Flower I love you too.” Dad’i sosai taji ta sake matse jikinta a nasa ahaka har sukayi bacci. ***** _7:30PM_ Tun idar da Sallan Maghrib da sukayi Fannah ta shjge kitchen ta fara aikin d’anwake acikin d’an k’ank’anin lokaci tagama ta had’a musu dining table tayi serving kowa a saucer, Anas na ganin haka ya saci jiki ya koma d’aki ya miqe kan gado shi a dole yana bacci bare chi d’anwake ba. Har d’akin ko ta biyosa “Habeebi tashi muje dinner is ready.” tayi maganan lokacin da take tsaye akansa, shiru yayi tare da sake gamme idanunsa shi wai adole yana bacci. “Baby tashi mana” ta gwada jijjik’ashi “meneh?” Ya tambaya sleepishly. “Baby wai bacci kake? Yaushe ne muka tashi daga bacci har kake wani? Tashi muje kaci abinci yaso seka dawo ka cigaba kaji?” “Banajin yunwa Flower.” “Nasani hak’uri zakayi karfa ya huce yayi sanyi tashi kaji My Lion.” Badan yanaso ba ya mik’e yabita bayan sun zauna ta ja mai saucer’n sa gabansa “bismillah lets eat” nan da nan ta soma kai nata ciki shide kallon saucer’n nasa kawai yake seda ta kusan rabin nata taga Anas beko tab’a nasa ba. “Habeebi inzo in baka ne?” “A’a chi naki zanchi da kaina.” “Toh chi mana ai yamayi sanyi” fork ya d’aga yasa ciki tare da danno kan d’aya seya kai baki seya sake maidoshi baya da abin ya isheta seda tabari yakai baki sannan ta tura hannunsa yasa d’an waken ciki yana fara k’ok’arin fito dashi a girgiza masa kai “karkayi please gwada chi mana kaji kaikam.” Tsotse zak’in jikin yayi kap ya jawo plate ya tufar da d’an waken akai. Kallonsa kawai ta tsaya yi cike da mamaki, wasu biyun ya sake kaiwa baki yana gama tsotse zak’in se ya fito dasu ya ajiye. “Wai Habeebi me haka? Haka ake cin d’anwake? Ai wannan almubazaranci ne.” “Kefa kikace senaci yanzu kuma da nake ci kina min surutu.” Nan ya cigaba da abinda yakeyi, ganin yakusan kai rabin saucer’n tace, “Baby kabari mana” sake matsowa kusa dashi tayi ta danna kan d’aya ta kai masa baki gashi karb’a ba musu ya karb’a “kuma karka tsotse Baby ka tauna ka had’iye.” “I can’t.” Ya sanar da ita. “Yes you can” ta tabbatar masa. Bayan ya gama tsotse zak’in yafara k’ok’arin cirowa aiko ta rufe mai baki “Baby ka tauna ka had’iye mana ko so kake yunwa ya soma damunka? Had’iye.” Kai kawai yake girgiza mata aiko daram ta zauna kan cinyarsa “yau seka had’iye in ba haka ba...” ta matso kusa da kunnensa ta rad’a masa abu ai take ya gyad’a kai. “Goood thats my Man” anan ta sake mai baki. Goran ruwa ya jawo kamar yadda ake had’iyar magani haka ya had’iye d’an waken haka yabi sauran yariga had’iyesu sekace meshan magani. Ita de Fannah nata ido ne. Bayan da suka gama dinner ta d’anyi assisting nasa wani aikin da yakeyi se 10:30PM suka kwanta. Washegari Anas yace sam bazasa office da jan goshi bah ba yadda Fanah batayi dashi ba yafa ce shi ba office da zeje haka suka sha baccinsu se to 11 suka tashi sukayi wanka tayi musu d’umamen as promised sam Anas yak’i chi ba yadda batayi dashi baya da yachi yace bare chi ba sede in fresh new one zata dafa bayan ta karya ta masa nasa breakfast daban kasancewar wheather’n garin yayi cloudy ba rana yau yasa suka fita baya wajen garden suna shaqatawa suna hiran masoya gwanin sha’awa abinsu. Honk da ake tayi yasa Anas ya miqe ya duba ko suwaye ne ganin motar Shettima yasa ya danna wani button gate d’in ya bud’u musu duk suka d’uru sukayi ciki. Amal da ba’asan an girma ba chak ta d’ale cinyan Anas tasa Ummie kunya. “Haba Amal ya haka kuma? Sauqo kinji?” Tana maganan tana kallon Fannah. “Ayyah Ummie barta ba komai she missd him thats why.” “Laaaaa Ya Anas me haka a goshin ka?” Cewar Amal nan hankalin kowa ya koma kan goshin Anas a tare Shettima da Ummie suka ce “dagaske fa amma meya samu wajen haka yayi pink?” Hannu yasa ya rufe goshin tare da bin dukkaninsu da kallo yana nazarin wani k’arya ze had’a musu idanunsa na had’uwa dana Fannah ta kawar dakai se k’ok’arin maze dariyan dake san kub’uto mata take. “Kayi shiru Anas” cewar Ummie “meya samesa Fannah?” Ta yi redirecting kallonta zuwa Fannah. Nan ta soma raba ido dan batasan me zata ce dasu ba. “Ermm... Erm-” katse ta Anas yayi. “D’azu ne zuma suka harbeni a garden ina d’an gyaran wani flower.” “Eh zuma suka harb’esa d’azu” ta mara masa baya. “Ayya sannu” duk su uku suka ce alokaci d’aya Amal na tab’awa yaja hannunta “da zafi stop it.” “Sorry.” Hira suka sha sosai da Fannah tama Ummie tayin d’umamen kuwa tace akawo mata haka suka zauna ita da Shettima suka narki tuwon banda Amal dake nan kamar Anas itama wai batachin miyan kuka se bayan Azahar suka tafi. **** “Kai aman gaskia Habeebi ka iya had’a k’arya sosai fah” ta kwashe da dariya. Banza da ita yayi. “Habeebi is a liar.” Wani kallo ya watsa mata “ki ka sake kirana liar sena miki abinda baki tsammani Flower.” “Do your worse” tamasa gwalo “My Baby is a liar” da gudu ta wuce kitchen tasa lock a duka k’ofofin se dariya take masa. “Ai ba kwana zakiyi ciki ba, zaki fito ki sameni.” Ya fad’a mata. “Zakachi miyan kub’ewan?” “Bansani ba kikayi abinki ke kad’an ki zakichi.” “Nida Baby na zamuchi.” “Babyn da one day zaki haifa ba amman bani ba.” **** A d’aki ta samesa da laptop gabansa yana d’an aiki. “Baby fito lunch is ready.” “Banajin yunwa.” “Tun safe banda chips da kachi me ka sake kachi?” “Toh laifin wa? Ba kece kike ajeni da yunwa ba.” K’arisowa d’akin tayi ta zauna kan cinyansa tare da zagaye hannayenta a wuyansa. “Kamar ya Baby? Ni ke ajiye ka da yunwa?” “Eh manah tun jiya kike dafa kalan abincin da bana chi kuma kin sani.” “Baby ai so nake ka saba bahaushe yace ba kullum ake kwana kan gado ba yanzu for instance in one day kaje Bama ina zaka samu irin abincin nan daka saba chi? ” “Even still je kichi abincinki ni baran chiba.” Gajeren hot kiss tamasa sannan tayi pecking nasa a kumatu “tashi muje kaji Habeebi na?” Besan a lokacin da yatashi ya bita ba ita da kanta take basa, ba kamar jiyan ba yau yaci kub’ewan sosai sabida yamasa d’and’ano bayan sun k’are chi suka koma d’aki tayi assisting nasa aikin dayake kai. _10:20PM_ Daidai nan Fannah tagama canzawa cikin wani had’ad’d’en rigan baccinta Anas kuwa akan nickers nasa da vest as always seda ya bari ta kwanta sannan ya hauro gadon ya had’e hannayenta gu d’aya “wa kike kira da liar d’zu?” “A’a ba kai ba.” “Nide nine liar ba?” “A’a Baby ba kai ba dan Allah kar ka min cakulkuli wallahi ba kaiba please karka-” bebari ta k’arisa maganan ba ya fara mata cakulkuli dariya take tana hawaye sosai tana had’asa da Allah sam yak’i bari. Seda ya tabbata ta galabaita sannan ya sake mata hannu ya share mata hawayen. “Next time zaki sake kira na liar.” Se “wayyo cikina” take tayi har a yanzu. D’agota yayi ya kwantar da ita jikinsa seda tagama dawowa hayyacinta ta d’ago kanta “Liar nasake fad’a” bata bari ya soma mata cakulkulin ba ta rufe sa da kiss sun d’au tsawon lokaci suna abu d’aya har wani su juya nan su juya chan suke alokaci d’aya Anas yasoma fita hayyacinsa dan wani irin kisses da Fannah ke masa kamar yadda shima yake mata all over her face and neck, duk sun zurfafa suna romancing junansu. Yasani in beyi stopping kansa ba yanzu he can’t later in kuma hakan ya faru zeyi breaking mata promise daya d’aukar mata before nacewa seda yardan ta abu ze gudana tsakaninsu. Da k’yar ya iya ya tashi daga kanta yaja baya ya zauna. “Baby meya faru?” ta tambayesa cike da damuwa tana k’ok’arin miyar da hannun rigarta daya fad’i sannan ta matso kusa dashi ta zagaye hannayeta daga bayansa. “What is it Habeebi?” “Babu” ya amsata blankly. “Da akoi Baby tell me.” A hankali ya cire hannayen nata ya juya yana fuskantar ta. “Flower I can’t go further... I..” Sekuma yayi shiru. “Why can’t you Habeebi?” “Flower kin manta promise dana miki seda concent naki zan tab’a ki?” Kai ta kad’a nufin ta tuni. “Kinga in ban tsayar da kaina yanzu ba I can’t later lets just sleep.” “No Baby I’m ready for it.” Ido ya zaro cike da mamaki yana kallonta “Flower me kikace?” kad’ai abinda bakinsa ya iya furtawa dan yadda mamaki ya rufesa. *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:58, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 7⃣7⃣ Wajenta ya nufa ya tab’a body tempreture nata nan yaji ya d’anyi rising. “Flower bakida lafiya” yayi concluding. “Habeebi kawai stress ne bawani abu ba.” “Wani aikin kikeyi in natafi? Ba girki bane kawai? Toh wani stress kike nufi Flower? Tashi muje asibiti sekace me sleeping sickess ko da yaushe bacci.” Juyowa tayi tana kallonsa “Baby wai me haka? Yanzu bacci ma barin iya yiba sekace seka kaini asibiti? Lallai fah Allah kacika bin diddigin abu, nikam ma inda zani” tana kaiwa nan ta juya tacigaba da baccinta kallonta ya tsaya yayi sannan ya zagaya ya sameta suka kwantan tare. “Flower I’m sorry didn’t mean to upset you.” “You didn’t my Lion nima I’m sorry.” “Your Lion is hungry.” “Baby kaifa kace kachi abinci a meeting yanzu kuma kana jin yunwa?” “Flower bana son tsiya fa sarai kinsan kalan yunwan da nake nufi feed me.” “Ni gaskia bansani ba” tana kaiwa nan ta juya masa baya chan k’asa-k’asa tace “mutum sekace sex machine ni barin iya ba.” Murmushi sosai ya saki lallai kuwa rabuwansa da ita 2 days now shine take wannan magana? “Nafa jiki Flower najiki da kyau kuma fushi zanyi.” Take ta juyo “a’a karkayi dan Allah yanzu bacci nakeji kabari ko anjima yi hak’uri lets sleep yanzu koh?” Shiru... “Koh Habeebi? Wallahi ji na nake ba k’arfi” Kai ya gyad’a mata ta matso kusa dashi ta kwanta. **** Bayan sun idar da Maghrib Fannah ta wuce kitchen dan soya musu scrambled egg a yayin da Anass ke parlour as ysual da laptpp nasa, tana cikin fasa k’wan d’aya ya fad’i ya fashe a k’asa aiko take kitchen d’in ya soma k’arni kafin ta hankara taji bakinta ya cike da amai. Guest toilet ta ruga a guje nan Anas dake parlour shima yabi bayanta. “Anas please karka shigo ka tsaya daga chan” ai kaman shigo tace masa ya k’ariso ciki yana shafa mata baya a hankali se aman take tayi se datayi sosai sannan ya taimaka mata ta wanke bakinta suka fito idanunta se wani kafewa suke a kan 2 seater suka zauna. “Flower whats wrong? Nafa fad’a miki bakida lafiya.” “Baby k’wai ne ya fashe so se k’arnin ya fitine ni dalilin aman kenan if not ba abi-” bata k’are maganar ba ta fad’a jikinsa dan wani jiri datake ji yana d’ibanta ko a zaunen ma. “Baby hold me kaji?” ta buk’ace sa. Hannayensa ya zagaye a bayanta “I’m here karki damu” bayanta ya riga shafawa up-to-down na zuwa wani lokaci. “Flower” ya kira sunanta shiru yana leqa fuskarta yaga tayi bacci mamaki ne sosai ya rufesa Ipad nasa ya jawo ya sake daidaita kanta a k’irjinsa sannan shikuma ya kishingid’a jikin kujerar. Nan ya shiga google yasoma browsing abubuwan dake jawo yawan bacci dakuma amai abubuwa da dama ne suka fiffito masa wanda one by one yake bi yana karantawa dayazo kan wani point seya tsaya yana nazari sekuma ya dawo da kallonsa kan Fannah “it might be true ban tab’a neman Flower tak’i ba se d’azu itan da sometimes ma take nema da kanta, ga wani kasalan da takeji dashi 2 days, ga baccin asara dakuma amai. Flower are you pregnant?” Ya tambayeta chan ciki-ciki. “Kai anya? Na kusan zama DADDY kenan?! Flower!” yayi whispering a kunnenta “na’am” ta amsa. “Please Baby barin d’an kwanta kad’an wallahi I’m weak.” “Kiji nace when last kika ga period naki?” “Baby meya kawo maganan period d’ina kuma anan? Dan Allah barni in kwanta” matso rigarsa tasakeyi a hannunta tare da sake daidaita kanta kan k’irjinsa ta cigaba da baccinta. Duk wannan magana da take kuma idanunta a rufe suke. Jijjik’ata yayi seda ta mik’e ta zauna. “Ohhh! Habeebi meneh?” Ta k’arisa maganan tana k’ok’arin zama, idanunta da take ta k’ok’arin bud’esu kuwa se kafuwa suke. “Good kinga period naki watan nan?” “Mesa kakeson sani?” “Flower mesa kike rashin ji ne waikam? Two days se misbehaving kike kode shima yana cikin symptoms d’inne?” Ya tambayi kansa kasancewar tana kusa dashi yasa tajisa. “Symptoms name Habeebi?” “Bansani ba ki amsani first.” “Babu bezo ba amman nasan sooner or later zezo saboda atimes haka yake min, se yayi skipping 4-5 days.” “Kin tabbata?” “Eh mana shikenan? Zan iya komawa baccin?” “A’a kitchen d’infa? Wa zeyi mopping wajen da egg d’in ya fashe?” Fuska ta maraice “Baby wallahi k’arnin amai yake sani kuma ma banjin inada k’arfin mopping inaji na ba k’arfi ko kad’an ji nake kamar nayi aikin d’aga block please kabari gobe in masu aiki suka zo senayi kaji Baby?” “Another symptom” yace da kanshi nanma ta jisa. “Wai wani symptom Baby?” “Flower look at me” nan ta maido da kallonta a agaresa. “Don’t you think you are pregnant? Mun kusan zamowa Daddy and Mammy?” Cike da rashi yarda tayi maganan, “Kana nufin wai ciki ne dani?” Ta k’are maganar hannunta kan flat cikinta, hannun sa shima yabi ya aza akan nata dake cikinta “sosai ma kuwa Flower karanta nan kiga” nan ya miqa mata Ipad d’in data gama karantawa kuma setaga almost all yadda take feeling haka aka yita bayani ciki toh ko dagaske ne tana da ciki? Ta kusa zama Uwa kenan itama? “Flower what do you think?” maganarsa neya tsamota daga tunanin da takeyi. “I think yes!” Ta fad’a delighted cike da jin dad’i. “I think so too Habeebi I might be pregnant!” “Yes Flower” hannunta yacire daga cikin nata ya sa nasa kai “we have a baby in here.” Hannunsa ta cire ta aza nata kan cikin “tsaya let me feel it.” “No!” ya zare hannunta ya d’aura nasa kai “ki tsaya inyi feeling first bani ne babba ba?” Nan ta sake cire hannunsa “sekaci girma ai kabarni inyi feeling nasa first, nida ciki na abeg d’aga min hannunka.” “Cikinki ko cikinmu?” Haka suka tayi Anas yak’i cin girma yabar Fannah ta fara feeling Babyn nasu kamar yadda itama tak’i cin k’ank’anta. Seda tagaji ganin Anas baida niyan barinta kawai ta barsa yafara feeling hannunsa yafi minti biyu kan cikinta yak’i d’agawa. “Toh ai haka yayi nima let me feel my Baby.” “Flower Allah kika sake cewa Babynki zamu b’ata. Its our Baby.” “Toh our Baby, kasan meh?” Kai ya kad’a mata. Matso da kansa tayi ta rad’a masa wani abu a kunne. “LOL yes I am Flower, so gobe zamuje asibiti?” “Muje muyi meh kuma Habeebi?” “Muje mu tabbatar da cikin naki mana ayi scanning.” “Shine se munje asibiti? “Yes Flower.” “A’a nikam barinje ba zan saya pregnancy test strip in gwada da kaina a gida ba se munje asibiti ba.” “I know Flower but still yakamata muje kinga zamu san how many weeks ne pregancy nakin and za’a bamu shawarwari dayawa kinga this our first time.” “Nikam gaskia Baby kayan kunyan nan badani ba.” “Wai wani kayan kunya Flower? Ciki abin farin cikin ne kuma abin kunya yanzu?” “Eh mana Baby kowa de yasan ta yadda ake samun cikin nan ni kawai mu rufa wa kanmu asiri kar muje.” Dariya sosai ya tsaya yanayi “Flower you are too much to meh? Suma haka akayi aka haifesu kowa ma haka akayi aka haifesa I see nothing wrong with that.” “Nide ba ‘yar iska bace barin jeba” tana kaiwa nan ta mik’e aiko seconds talatin batayi ba ta fad’a kujeran ta dan jiri da sauri ya taro ta. “Flower fa dole muje asibiti final decision.” Chak ya d’agata yakaita d’aki black tea ya had’o mata bayan tasha yajasu Sallah wanda rabinsa ma a zaune Fannah tayi dan jiri. _Washegari..._ Asuban fari Anas ya tashi bayan yayi alwala ya taimakawa Fannah ma tayi suna idar da Sallah suka koma suka kwanta sede unlike jiya yau jikin nata da zafi amman ba chan chan ba gudun karwani abu yasamu lafiyan babynsu yasa Anas yabata paracetamol kad’ai tasha cikin ikon Allah yamata aiki kuwa, k’arfe shida ta tashi as always taje ta had’a musu breakfast hancinta toshe da hanky dan gudun k’arnin fashasshen k’wan bayan tagama ta jera dining sannan taje ta tada Anas. “Baby katashi kayi wanka kaji?” Bayan ya bud’e idanunsa ya k’are mata kallo bakomai ne d’auke a idanunta ba banda kasala. “Flower kinyi wani aiki neh?” “Breakfast kawai na shirya mana se ruwan wankan ka tashi kashiga.” “Flower why? Daga yau banason ki sake yin wani aiki kinji? Its not fit for your condition.” “Baby bamu ma tabbata ko cikin ne dani bafa tashi kayi wanka” towel nasa ta mik’a masa nan danan yayi wanka yashirya sannan yafito suka fara breakfast kad’an daga cikin fried egg d’in Fannah taci ya sata amai aguje ta ruga bathroom shima Anas yabi bayanta yana shafa mata baya, amai ta rigayi abin tausayi, data gama ya tayata kimtsa kanta suka fito tana manne a jikinsa dan jiri. “Flower bara muje asibiti ba?” Kai kawai ta iya ta gyad‘a mai. “Sorry kinji? I can’t leave you alone like this.” “Me kake nufi Baby?” “Nafasa zuwa office I will take care of you.” “Common Habeebi karka damu I will be fine je ka gama breakfast naka kaji? I love you” peck ta manna masa a kumatu da k’yar tare da komawa ta lume cikin kujeran. “Flower in kaiki d’aki?” “Nanma yayi kayi sauri.” Mik’ewa yayi yaje d’aki yafito da blanket bayan ya kunna AC ya lullub’eta dashi sannan yayi pecking nata a goshi. Dining ya koma yayi rushing ya gama breakfast nasa, wayarsa ya d’aga dan kiran Kacallah ya fad’a mai bazasa office ba yau yaga Kachallan na kiransa. Bayan yayi picking Kacallah ya gaishesa “Sir na kira ne dama in tuna maka meeting da zakuyi da board of directors na F&C Enterprises regarding 2% shares nasu da zasu siyar mana dakuma investing da zamuyi.” Kallon sa ya miyar kan Fannah ji yayi bare iya barin ta haka ba dan kuwa batada lafiya. “Hello Sir?” Cewar Kacallah dan jin shiru. “Kacallah baraka iya presenting d’ina ba? My wife is sick I’m afraid barin iya barinta ita kad’ai ba.” “Ayya my regards please kuma Allah ya sawaqa unfortunately I can’t Sir dole se kai in ba haka ba barasu siyar mana ba kuma kasan we can’t lose this oppurtunity please Sir.” “I will see to it” nan yayi hanging. Wajen Fannah ya nufa ya zauna a gefenta. “Flower” ya kira sunanta. “Na’am” ta amsa a kasalance. “How are you feeling? Ki fad’a min tsakanin ki da Allah karkimin k’arya.” “Baby kasala ne kawai sekuma zuciya na dake yawan tashi thats all.” “Bakiya feeling feverish? (zazzab’i)” “Kad’an ba.” Ta amsa shi. “I can’t leave you like this zanyi canceling meeting d’in.” “Wani meeting Baby? Bade na F&C Enterprises ba!” “Shi Flower barin iya barin ki haka ba.” Juyowa tayi tana fuskantanshi “please kar kayi haka kaji? Karkayi losing wannan oppurtunity, karka damu dani in nasamu na kwanta I will be fit.” “Kinsan fa ba ke kad’aice ba yanzu akwai little one namu.” Wahallalen murmushi ta saki “don’t worry I’ll take care of it for its Daddy, off you go kaji? Best wishes I love you.” “I love you too Flower” yayi maganan yana gyara mata blanket d’in “take care of yourselves for me ko in kira Afrah tazo ta tayaki zama?” “A’a karka damu I can manage.” “Sure Flower?” “Yes Baby.” Brushing light kiss ya mata a baki “I love you okay? Ki kirani in wani abu na daminki kinji?” “Yes Sir!” ta masa murmushi har ya miqe sekuma ya dawo ya zauna “kinga banyi greeting baby naba” hannunsa yasa cikin kayanta yashafa kan cikin. “Good morning my baby your Daddy loves you so much.” Murmushi kad’an ta saki dukda kuwa yabata dariya sosai. “Habeebi nothing is certain yet fah kar muta hoping muzo kuma abu yayi turning out in a different way.” “I still don’t care, I love you bye.” Jakansa ya d’aga ya fice a yayinda ta rufe idanunta tare da aza hannunta kan cikinta tana shafawa a hankali da murmusi fal kwance a fuskarta. **** Sosai d’an baccin da tayi ya taimaka mata dan kuwa ta samu k’arfin jiki takuma warware, d’aya daga cikin masu aikin nata ta aika chemist ta siyo mata strips guda biyu, bayan ta kawo mata tashiga toilet tayi carrying out test d’in se bugawa zuciyarta ke bayan daya gama reading ta bud’e ido d’aya da rabi ta leqa tana ganin ‘P’ ta bud’e duka nan ta karanta ”POSITIVE” ta karance. Tsalle ta daka “yeyyy!!! I’m pregnant!! I’m pregnant!!” A gurguje tafito daga bayin ta d‘au wayanta ta kira Anas sede har ya yanke be d’aga ba kasancewar yana a meeting 2 missed calls tamasa ganin be d’auka ba tamiyar da wayar ta ajiye. 1:50PM lokacin da Anas yafito daga meeting d’in ya duba wayarsa yaga missed call na Flower ba tare da b’ata lokaci ba ya kirata back daidai lokacin da take fitowa daga wanka kenan a dole tayi zuciya tak’i picking se a karo na biyu ta d’aga nan ma tak’i cewa komai “Halo Flower?”,nanma shiru. “Flower don’t be mad I was in a meeting kinji? Yi hak’uri kimin magana.” Se anan ta sauk’o. “Ya meeting d’in?” “Alhamdulillah yanzu muka fito, ya jikin ki?” “Da sauk’i me kakeso kachi yau?” “Babu karki dafa komai zan saya mana lunch banason kina wani aiki yanzu.” “Hunmm! As you say Mr. Fauzi yau inada suprise maka.” “Really Flower? I hope ba irin suprise na miyan kukan da kika min ranan bane?” Dariya ta saki “ko kad’an Habeebi” “Toh tell me meh suprise d’in?”,Baki ta cuno. “Suprise nefa Habeebi ai ba’a fad’a seka dawon de, k’arfe nawa zaka shigo?” Rolex agogon hannunsa ya duba “erm... Zuwa 3 haka.” “Okay toh sekazo.” “Wait.. Wait fad’amin kinji meh suprise d’in? Ko hint ne kibani.” “O’o seka dawo I love you!” Bata jira ya sake magana ba ta katse wayar tana murmushi shima murmushin yake. Had’ad’d’iyar kwalya ta tsara tasa wata had’ad’d’iyar light purple lace da torches na fari da dark purple d’inkin peplum da skirt. Bayan nan ta kafa d’aurin network nata me kyau sannan ta feffeshe da turarukan ta meh yima Anas dad’i. Game ta zauna tata bugawa chan takira gida suka gaggaisa. 3:15PM nayi ta b’allo sabon strip ta sake carrying out test d’in ta ajiye 3:20PM Anas ya dawo gida k’ofa na bud’uwa Fannah ta bayyana a bayansa kallonta yake wane a mafarki sekace ba itace ke kwance ba lafiya ba d’azu. Another symptom yace a ransa morning sickness. Bayan ya shigo ya miyar da k’ofan sannan ya juyo yana kallonta har a yanzu tunanin wani kalma ze furta wanda ze dace da kyan da Fannah tayi yake. “Flower you are looking extra ordinary spectacular, you’re looking amazing.” “Thank you Sweetheart” ta fad’a tana mai murmushi matsowa kusa dashi tayi seda ta rufe gap dake tsakaninsu nan k’amshin jikinta me haukatasa ya buga masa hanci besan alokacin daya fara bin wuyanta yana shunshunawa ba. Hannu tasa ta shuresa da k’yar “Baby waittyy manaaa” bata bari ya sake komawa jikinta ba ta mik’a masa strip dake hannunta. “What is this Flower?” Ya tambayeta. “Pregnancy test strip.” “Kina nufin har kinyi carrying out test d’in without me?” “Yes Baby I’m sorry duba kaga result d’in.” Da hanzari ya maida kallonsa kan bar d’in “POSITIVE” yaga rubuce kai. *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:58, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 7⃣6⃣ Hannunsu ta had’a tana murzawa a hankali, “I’m ready Habeebi.” Har yanzu ya kasa yarda, “Flower are you sure?” Kai ta gyad’a “I am Habeebi.” “No kawai fad’a kike Flower kinbar tsoro na?” D’an dariya ta saki “tsoronka? Aini bana tsoronka.” “Are you sure?” Ya sake tambayarta yana d’age mata gira d’aya. “Bakiya tsoro kar nayi destroying naki na saki kuka?” “Kukah! Adalilin me zanyi kuka ko ka manta am not a virgin” bata jira ya sake magana ba ta jawo sa ya fad’a jikinta ta cigaba da kissing nasa yana meh mayar mata da martani, hannu ya mik’a yayi switching off wutan d’akin. (Ba halin d’auko rahoto se Fans suyi hak’uri. LOL) Chan de na d’anji k’aran Fannah ai bada jimawa ba ta soma ihu tun tanayi kad’an kad’an zafin ya fara mata yawa. Ko Habeebi da Babyn ma babu yanzu. “Anas I’m not ready dan Allah kabari wallahi I am not wasa nake maka I don’t mean it kabari please.” Ko kad’an Anas be saurara mata ba dan kuwa gabad’ai ya riga yafita daga hayyacinsa. “Wayyoo Allah Mami!! Anas zaka kasheni wallahi I’m not ready please I’m sorry” se hawaye shark’af shark’af take. “Mr. Fauzi please kadena dan Allah kayi hak’uri barin sake forcing naka cin tuwo ba na tuba dan Allah!!!” Ba kalan suratan da Fannah batayi ba a daren ranan, tana me ma Anas rok’an duniya amman ko kad’an Anas be saurara mata ba seda ya gamsu tukunah, anan ne ma yasoma jin sautin kukan datake ta rerawa a hankali tsabagen yadda k’arfin jikinta ya k’are a shurin Anas data tayi, dande bata da faracu ne da Anas yasha yak’ushi kam. Matso ta gam yayi ajikinsa wane za’a k’wace masa ita se kissing gashinta yake yana suburbud’a mata albarka. Har a yanzu sarkin kukan datace she is ready bata bar kuka ba haka yata bubbuga bayanta har seda yaji nauyinta a jikinsa ya dad’u tabbacin tayi bacci kenan se anan shima ya samu yayi baccin. Asuban fari ya tashi a hankali ya raba jikinsa da nata sannan ya fad’a bathroom yayi wankan sunnah tare da d’auro alwala ya had’a mata warm wata cikin jacuzzi sannan yafito bayan yasa jallabiyansa ya koma ya zauna gefen Fannah dake ta bacci har a yanzu, fuskarta duk jirwayen hawaye murmushi sosai wanda ya sake lotsar da dimple nasa had’e da k’ara masa kyau ya sakar se anan kalamunta suka fara masa yawo akai. “Flower” yayi wispering a kunnenta a farko bata bud’e idanunta ba se a karo na biyu. A hankali ta soma bud’e idanun nata har tagama bud’esu, kyakkyawar fuskar Anas ne yasoma mata sallama pillow taja ta kare fuskarta. D’an murmushi ya saki. “Flower good morning.” Nanma bata tanka saba, daya gwada sa hannunsa cikin blanket d’in kuwa setayi sauri ta tattara ta mammanne a jikinta. “Flower tashi kiyi warming jikinki kinji? Bamuyi Sallah bafah.” Nanma shiru. “Flower baraki min magana ba?” Nanma shiru. “Seda fa na fad’a miki I’m a Lion kika ce you are still ready yi hak’uri ki tashi.” “Toh ai daga baya nace maka kabari I’m not amman kak’i ji na.” “I’m sorry toh yi hak’uri ki tashi.” “Naji excuse me in nagama komai zan kiraka.” “Are you sure barakiyi needing assistance d’ina ba?” “Eh kafita please.” Hannu yasa ya cire pillon data rufe fuskar nata dashi “kabani” ta fad’a idanunta a rufe kamar wacce zatayi kuka. Peck ya manna mata a goshi “I love you Flower” k’in replying nasa tayi seda taji ya fita sannan ta bud’e idanun nata sewani tura baki take kayanta dake a k’asa ta d’aga tasa a kasalance sannan ta gwada tsayawa sam takasa da k’yar d’in k’yar tana dafe-dafe ta isa bayin ta shiga, ruwan daya tanadar mata ta gwada shiga nanma se k’ananun ihu take sakarwa sam ta kasa shiga, zama tayi a gefe guda tana kuka ita ta d’au ai tunda this is not her first time barataji komi ba ai duk laifin Mami ne data sani gaba tariga bani wasu jik’e-jik’e. Anas dake tsaye bakin k’ofar d’akin yana jirarta daman yasan ba abin arziki Fannah zatayi ba jin shiru yasa kai ya shiga. D’akin ya duba be ganta ciki ba chan yaji sautin kukanta a bayi da hanzari ya k’ariso bakin k’ofan. “Flower why are you crying?” Tana jin muryarsa ta share hawayenta tare dayin kum da baki. “Flower meya faru? In shigo?” “A’a karka shigo dan Allah.” “Toh kinyi wankan?” Data kalli jacuzzin seta sake b’arkewa da kuka dan batajin zata iya shiga wai ruwan yamata zafi. Take Anas ya bud’e k’ofar ya shiga. Baya ta juya masa da wuri “Anas ka fita banaso ba kyau dan Allah ka fita” ko sauraranta beyi ba ya d’agata chak kamar ‘yar Baby ya tsunduma ta cikin jacuzzin, zafi sosai taji ta sakar da wani erin k’ara tare da matsesa jikinta gagam ta riqesa tak’i sakesa seda jikinta yasaba da ruwan d’umin tukuna. A kunyace ta sake sa ta soma kare k’irjinta tana kallon k’asa. “Zakiyi wankan ko in miki?” “Anas wani erin magana ne? Taya zakamin wanka ni ka fita dan Allah banaso.” “Anas kad’ai yau ba Baby ba Habeebi bakuma Lion?” “Ai kafi Lion mugunta Hyena ne kai nikam kafita min.” Murmushi sosai yakeyi “kiyi sauri ina jiranki” yana kaiwa nan ya fice. Binsa tayi da kallo sannan a hankali tasamu tayi wanka tayi alwala tafiya d’ai d’ai takeyi har tafito. Zaune ta tarar da Anas kan gado tafiyarta tayi k’ok’arin daidaitawa amman sam ta kasa dan zogin da takeji, miqewa yayi ya k’ariso da ita kan gadon ya zaunar da ita tare da d’auko mata lotion nata. “Baby me zakayi?” “Shafa miki.” “A’a nikam banaso zanyi abina dakaina” hannu tasa ta karb’e. Kallonta kawai yake seda yabari tasa man a hannunta sannan ya kama ya kwashe man kafin tayi magana ya fara shafa mata man. “Anas kabari its embarrassing.” “Dan ina shafawa Flower na mai shine abin kunyan?” “Eh mana” ta gyad’a masa kai. Bayan daya gama shafa mata ta masa godiya sannan ta mik’e tasa wata simple doguwar riga bak’a. Suna idar da Sallah suka koma suka kwanta se anan tayi noticing chanza bedsheet da Anas yayi. “Habeebi kai ka canza bedsheet d’in?” “Yes Flower” ya amsata lokacinda yake kwantar da ita kan k’irjinsa. “Dama ka iya changing bedsheet?” Murmushi kad’an yayi “meh kika maidani ne wai Flower?” “Ajebo mana, ajebon da be iya komai ba ma.” “Nine ban iya komai ba?” “Eh mana toh me ka iya?” “Na iya sa Flower kuka, na iya changing bedsheet and na iya girki.” “I agree with number two amman ban yarda da number one and three ba dan ni baka sani kuka ba” “LOL aikua harda majina ma nasaki” “Hyena kawai” “Ko baki yarda ba yanzu in sake saki wani kukan?” bugu takai masa a k’irji “mugu kawai” dariya sosai yake “when will you be ready next?” “Ready? Chab! wallahi na tuba ba ruwana dan Allah kar ka sake” “LOL Flower bade tsoro ba karki damu barin k’ara ba, I will suprise you today zan mana breakfast, me kuka kawai. Anas I’m not ready wayyo Mami” ya kwaikwayeta yana dariya. “Mschw! Seka tayi ai” nan ta tashi daga jikinsa takoma k’arshen gadon tare da juya mai baya. Pillonsa ya matso kusa da nata “nikam ka koma wajenka kabarni inji da abinda ke damu na.” “Meke damunki Flower?” “Bansani ba ai kafini sani Hyena kawai.” “Flower nine Hyena?” Kai kawai ta gyad’a masa “toh Flower I’m sorry.” “Naji lets sleep toh” hanunsa ya zagaye ta cikinta ahaka suka koma bacci. _11:16AM_ A hankali ta bud’e idanunta juyawanda zatayi taga ba Anas kan gadon k’ok’arin miqewa tayi sede ta kasa dan wani pain da take feeling yanzu har fiye dana da. Kuka ta soma tana kiran sunan Anas ko kad’an be jita ba dake yana chan kitchen yana garnishing masu breakfast. Louisiana me rai da lafiya ya musu yana tsaye gefen microwave yana jiran time d’in yayi ringing. Singlet neda vest baqi sanye jikinsa. Wayar sa dake kan counter ne yasoma ringing yana kai dubansa yaga Flower da sauri ya d’aga kafin yayi magana yaji sautin kukanta. “Baby please kazo” ta fad’a cikin sautin kuka, microwave d’in ya kashe sannan ya fita a gurguje kwance ya sameta kan gado se hawaye take “Flower whats wrong?” Ya tambayeta cike da damuwa yana share mata hawaye. “Baby zafi.” “Zafi a ina?” “A k’asa na.” “Okay sorry kinji? Sannu kinason muje asibiti?” “Asibiti? Se muje mu cemusu meh? Munyi wani abu kajimin ciwo? Gaskia ni bara’ayi wannan kayan kunyan dani ba, just help me in miqe.” Murmushi sosai ya saki ya taimaka mata yakaita bathroom ya had’a mata warm wata sannan ya bata space. Bayan fitowanta ta shafa mai sannan ta sa wani babban vest tsayinsa iya guiwa, gashinta ya taje mata yamata packing dakansa sannan ya takota da kansa yakaita har dining sannan yayi kitchen ya ciro musu louisiana nasu tun anan k’amshin yasoma bugin hancin Fannah duk tabi ta k’osa taga meya girka. “Wow!” ta furta lokacin da ya ajiye abincin kan dining kallon reaction nata kawai yake sannan yayi serving nata tana kai baki taji dad’insa sosai. “Baby meh sunan wannan?” “louisiana” ya fad’a mata. “louisiana” ta nanata. “Akoi dad’i ba?” “Ba laifi.” ta sake kai wani bite bakinta. “LOL yafi wannan shirmen miyan kuka da kub’ewan da kikeyin.” “Be fi ba kawai de ba laifi amman kad’an k’ara min mana yayi kad’an.” “Kefa kikace ba dad’i akoi miyan kub’ewan ki sena miki reheating.” “Haba mana Baby kasani kuka jiya kuma ka hanani abinci yau?” “Bafa hanaki nayi ba Flower tuwon kine in kinaso in miki reheating.” “Toh banaso louisianan nakeso kuma shi zanci.” Nan ta miqa hannu ta d’aga tray d’in seda ta cinye kap kallonta kawai Anas yake yana adoring nata bayan data gama ya b’allo mata pain killers ya bata ta sha. ★★★★★ Haka rayuwa ta cigaba da kasancewa wad’annan masoya guda biyu Anas da Fannah. K’ara san junansu suke a kowani second kullum suna maqale da juna in Anas yana gida ba ruwansu da wani fad’a. K’imanin wata d’aya da sati biyu kenan yanzu koda Fannah taga period nata yayi missing bata kawo wani abu a ranta ba saboda daman haka yake mata atimes sede kuma yawan kasalan datake ji yanzu tun shekaran jiya da ta zauna se bacci kullum bacci. Da k’yar ta iya shirya Anas office yau se Allah Allah take ya tafi ta dawo ta kwanta haka kuwa bayan ta masa goodluck kiss ta rufo k’ofa ta dawo ciki ta baje se bacci ba ita ta tashi ba se kusan k’arfe d’aya nanma baccin be isheta ba dan de tasan zatayi girkin rana ne bayan tayi wanka tasa wani silky doguwar riga d’inkin booboo. Powder kad’ai ta shafa ta shiga kitchen sam batasan mezata girka masu bama parlour tafito se hamman yunwa da bacci take tayi. Fridge ta dosa ta bud’e taciro ragowar kazan da Anas yaci ya bari jiya, shi ta k’arasa sannan ta kora da ruwa amman sam seji take kamar bataci komai ba tana kurb’an fanta akai kawai seta jiyo amai guest toilet ta nufa a gurguje tariga kwararo amai wane zata harar da kayan cikinta bayan ta gama ta wanke bakinta abin tausayi tayi alwala sannan tayi Sallah, rashin sanin mezata dafa musu har yanzu yasa ta kira Anas. “Halo Baby” tayi maganan cikin wani erin kasalaccaccen murya. “Flower are you okay?” Ya tambayaeta cike da damuwa. “Eh meh ka gaka?” “Your voice sounds not okay.” “Babu karka damu nace me zakaci yau I can’t think of anything.” “Flower cook anything kinji? Karki damu I’ve got to go inada meeting I love you.” “I love you too” ta katse. Duban agogo tayi taga 10 minutes to 2 “barin d’an mik’e zuwa 3 haka se in dafa masa ko spaghetti.” tace da kanta. Throw pillow taja ta miqe kan 3 seater anan tasamu ta kwanta ba ita ta tashi ba 3:10PM brushing kad’ai tayi ta fad’a kitchen da wurwuri ta had’a markad’an ta aza kan gas nanma tana girkin tana kwanciya ahaka har tasamu tagama had’a komi sauran jiran nunansa kad’ai ta juye a flask ganin tagaji da tsayuwan ta dawo dining taja kujera ta zauna chan ta aza kanta kan table d’in aiko daga nan bata sake sanin ina take ba ruwan abinci kam har ya shanye Fannah batazo ta sauk’e ba da kad’an kad’an girki ya fara k’onewa duk anan bataji ba. 4:10PM Anas ya dawo gida tunda ya bud’e k’ofar yafara jin warin k’onuwan abu ko jakansa be ajiye ba ya nufa kitchen yayi turning off gas d’in se anan ya ga Fannah dake kwance a dining area tana sharb’an bacci. “Flower” yayi tapping nata anan ma bata tashi ba seda ya matso kusa da ita yakira sunanta cikin kunnenta sannan firgit ta tashi. “Ya Salam! Abincin ya k’one Baby sannu da zuwa” takama hanyan kitchen kenan ya rik’o hannunta tare da dawo da ita baya. “Baby ka sakemin hannu please abincin is burning.” “Na riga na kashe gas d’in Flower.” “Huh! Ya k’one koh?” Kai ya gyad’a mata. “Ya Salam! Habeebi I’m so sorry bansan meke damuna ba tun shekaran jiya banida aikin dayafi bacci yanzu me zakachi? Kuma kanajin yunwa koh? Tsaya ko indomie ne in dafa maka I’m sorry kaji Habeebi.” “Calm down Flower karki damu banajin yunwa naci abinci a meeting d’in da mukayi.” “Habeebi are you sure?” “Yes Flower, kinsan bakida lafiya kuwa?” “Mesa kace haka?” Ta tambayesa “You are weak Flower meke damunki?” “Baby babu bacci kawai nakeji.” “Akoi tell me.” “Seriously babu kawai amai kad’an nayi d’azu shid’inma nakega saboda gas dake cikin fantan dana shan ne, muje ka huta kaji?” Nan ta ja hannunsa sukayi d’aki bayan ta tayasa ya rage kayan jikinsa ta mik’e gado ta kwanta se bacci, bece da ita komai ba se 4:30PM ya matso kusa da kunneta yayi whispering. “Flower kinyi Sallan La’asar?” Cikin baccin ta amsa sa “banyi ba amman zanyi.” “Se yaushe?” “Yanzu” ta amsa sa. “Then tashi” haka da k’yar ya tada ta tayi alwala tayi Sallah kasancewar shi ya idar tun a office nanma tana idarwa ta koma baccin jikin Anas se basa yake Fannah ba lafiya ba tun shekaranjiya yake monitoring moves nata ba aikinta se bacci ga wani kasalan da take yawan ji. Toh meneh? Kode sleeping sickness ke damunta? Nide Miemie nace ciki ne ya kukace masu karatu...??? *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:58, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 7⃣8⃣ I dedicate this chapter to *FATY MALUMFASHI* for the love, I love you Habibty😘😘 Had’ad’d’un blue eyes nasa yazaro cike da rashin yarda dan jin dad’i, farin cikin da baya iya misaltuwa ne kwance karara a fuskarsa “Flower its positive! you are pregnant!” ya fad’a cike da jin dad’i. Jakansa da ledan abincin ya ajiye kan kujera tare da d’aga Fannah sama dan jin dad’i “Flower we did it!” Murmushi sosai take wanda ya sake qayata ta. Bayan da ya sauk’o da ita yayi pressing mata hot kiss sannan ya rik’o ‘yar fuskarta duk suna murmusawa, rungumota kawai yayi “thank you Flower thank you so much I love you and our little one.” “I love you too Hyena.” Bayan ya sakota ya had’e gira “bance miki banason sunan nan ba.” “LOL to ai Hyenan ne kai Father to our child.” “Lets eat Mammy to be.” Ledan abincin ta miqa hannu zata d’aga yayi sauri ya rigata “uh-uh” ya kad’a mata kai “banason kina aikin komai yanzu zan k’aro masu aiki harda chefs ko girki ma banason ki sake kinji Mammy to be?” “Baby ai gatan yayi yawa kod’an girki ne seka barni inayi.” “Banaso kinsan abinda nakeso dake?” Kai ta kad’a mai. “Abu d’aya nakeso dake just take care of yourself and our baby shikenan, zakimin?” “Ofcourse Habeebi.” Shi da kansa yayi serving nasu abincin suna ci suna hira gwanin sha’awa har suka gama d’aki ya shiga ya canza suit nasa yasa sweaty pants da longsleeve shirt sannan ya d’auko mata hijabin ta itama. “Baby zamu fita ne?” Ta tambayesa alokacin daya k’ariso cikin parlour’n. Be amsata ba seda ya sa mata hijabin tukuna. “Asibiti zamuje.” “Muje muyi me kuma? Ba gashi munyi test d’inba and its positive meh amfanin zuwa?” “Trust me Flower lets go no arguement” badan tanaso ba tayi shiru hannunta cikin nasa suka fice, isarsu asibitin keda wuya Fannah ta soma rigima ita barata fito ba da k’yar da lalashi yasamu ya fito da ita daman already ansan da zuwansu basuyi wani zaman jiran doctor ba aka kaisu d’akin sede Anas be d’au na miji neba doctorn acewarsa mace ce. Bayan sun gaisa yayi ma Dr bayanin komai sabida yasan bayi Fannah zatayi ba. D’an k’aramin k’ofan dake cikin office d’in Dr’n ya buk’aci Fannah data shiga bayanta Anas yabi suka shiga tare haka shima Dr’n, kan wani k’aramin gado dake a gefe guda a d’akin likitan ya buk’aci Fannah ta hau kafin ta miqe akai Anas ya dakatar da ita ta hanyan rik’e hannunta “Dr I don’t get it kana nufin kaine zakayi mata scanning d’in?” yayi magnar cike da rashin yarda. “Yes Mr. Fauzi this is something I do everyday karka damu.” “Inaaaa!!” ya fad’a yana girgiza kai. “A nemo female Dr kawai ba yadda za’ayi matata ta kwaye maka cikinta banaso.” (kishi ya k’osa) Dariya sosai yabawa Dr’n. “Toh nid’in acewarka banida mata ne? Ko bakasan har karb’an haihuwa inayi ba. This is my job.” “Oho bansani ba nide a nemo female Dr.” Fannah dake tsaye a gefensa ne tasoma jin kunyan abinda yakeyi shegen kishi sekace d’an k’aramin yaro. “Baby kabari please its embarrassing.” “No Flower its not nide barin bari ya gane miki ciki ba.” Dawo da kallonta kan Dr’n tayi. “Dr please I’m sorry, haka yakeda wawan kishi in akwai female Dr a nemo mana ita please I’m sorry.” Kai kawai ya kad’a sannan ya fice ya kira wata female Dr in less than 10 minutes ta iso se mita take jin an ambaci Mr. Fauzi tayi shiru ta fara fara’a. Shi da kansa Anas ya kwantar da Fannah ya kwaye mata kayan daidai cikinta sannan ya riqo hannunta cikin nasa yana kissing. Cikin scanning machine d’in aka nuna musu d’an d’ayansu wanda yake nan d’an k’ararrami kasancewar Fannah is only 5 weeks pregnant dan marmari har printing photo scan d’in seda sukayi har copies uku. Shawarwari da dama female Dr d’in ta basu takuma buk’acesu da suna zuwa on regular basis bayan ta rubuta musu ‘yan maguna. Godiya sosai sukayi mata sannan suka fice chemist siyan maganin tun achan nurse d’in tasoma yima Anas wani gane gane taga mutum da blue eyes aiko Fannah na noticing haka ta tura Anas ta amshe maganin da kanta shiko basarwa yayi, yi yayi kamar besan meya faru ba. Suna zaune cikin mota Fannah taciro photos d’in ta mik’awa Anas d’aya duk sun zurfafa suna kallon photo d’in daga bisani suka ce da juna “what do you think is our baby’s gender?” a tare. Murmushi duka sukayi “you go first” Anas ya buk’ace ta. “No you” ta amsa sa. “Okay nikam ban damu ba muddin mutum ne like us and zan iya kiransa ko ita Mini Fauzi alhamdulillah.” Dad’i sosai taji dayace haka ba kaman wasu jahilan maza masu cewa se na miji suke so ba basu san ‘ya mace. “Kefa Flower?” ya tsamota daga duniyar tunanin data wula. “Me too Baby I love our baby look at it.” Ta matso masa da picture’n se admiring babyn da basu san hannayensa ba bale k’afafunsa suke. A hanya Anas ya riga tsayawa yana siyawa Fannah kayan k’walama kasancewar female Dr tace masa mata masu ciki akoi su da kwad’ayi kuma ana iya k’ok’ari ana biya masu buk’ata. “Baby wai ina za’a kai wannan abubuwa ne?” “Nakine dana babyn mu in ke bakiso shi ko ita suna so.” Bayan sun iso gida ya cicciro komai da kansa be barta ta ta cire koda tsinke ba suna zaune a parlour suna shan ice cream Anas ya d’ago wayarsa dake kan centre table. “Me zakayi Habeebi?” “Zan kira Ummie in sanar da ita ne.” Take ta taso daga jikinsa tana zaro idanunta. “Ka sanar da ita meh?” Ta tambaya cike da rashin fahimta. “That you are pregnant.” Hannu tasa ta wabje wayan. “A’a wallahi bara’ayi kayan kunyan nan dani ba.” “Flower wai wani kayan kunya?” “Ai kafini sani dawani idan kakeson Ummie ta fara kallo na? Ni gaskia kabari in cikin ya girma da kanta zata gani amman haka kurum ka hau kiranta kana fad’a mata inada ciki banaso” “Toh naji sarkin kunya Mami fa? Kawo in sanar da ita.” “Danqaree! ashe bakason na sake sa k’afa a gidanmu kenan ai in Afrah taji inada ciki I don’t think zata barni in sake shan iska.” “Kefa kike damuwa, kowa ta yadda muka bi aka haifesa kuma shima haka yabi ya haifi wasu, I see nothing wrong.” “Eh koma meh ni kar a kirasu.” “Toh Mrs. Fauzi naji yaushe zamu fita first shopping wa baby?” Ya k’are maganar tare da dafe hannunsa kan cikinsu (injisa da fad’i) yana shafawa a hankali. “Kai Habeebi yanzu cikin wata biyar za’a ma siyayya?” ta k’are maganan tare da kai spoon na ice cream bakinta. “Eh mana koda cikin kwana d’aya nema you just don’t know how excited I am nima nakusan zama Daddy.” Gira ta had’e wanda a dalilin haka Anas ya tambayeta ko lafiya. “Wani irin lafiya Habeebi? Bayan tun ban haifo baby’n ba ka fara nunawa kafi son sa fiye dani.” Kwashewa yayi da dariya “aww dariya ma nake baka koh?” “No Flower I’m sorry, I love you guys all kinji? You guys are my family ai kema kinsani duka inasonku kuma ma nafison ki tunda kece source d’in happiness d’ina.” Ya k’are maganan tare da placing mata peck a kumatu anan ne ta d’anji dama-dama. “Kuma Baby please kad’au min alk’awari baraka na biyewa ‘yan matan wajen nan ba kaga ko nurse na d’azun nan se kallonka take.” “Toh Flower taga Mr. Handsome ba dole ba.” yayi maganar cike da gatsine dakuma gira d’aya d’age. “Naji kuma nasani you are handsome and thats why am jealous of you banason ana gani mun kai haka.” “LOL Flower is jeolous.” “Habeebi I’m serious wallahi banaso” ta k’are maganan kamar wacce zatayi kuka. “Shhh! Baby Mamah karkiyi kuka hakan bare k’ara faruwa ba, I promise.” murmushi kad’ai ta saki masa. ***** Tun daga ranan Anas ya maida Fannah tamkar gold da ba’asan yasha wahala, ko aikin d’aga tsinke ya hanata yi ba aikinta se kula da kanta dakuma little one nasu. Wani soyayyan ma se a yanzu yasoma nuna mata kamar hauka fiye dana da bayasan komi ya tab’ata kullum hannunsa na akan cikinta yana feeling baby’nsu, Anas ya d’au son duniya ya d’aura wa cikin Fannah, ko kwanciya anyhow ya hanata wai shi kar ajima baby’nsa ciwo wani sa’in har haushi yake bawa Fannah dan abinda yakeyi itan da abu ke jikinta amma batada iko akai. A dalilin condition nata da rashin samun cin abincin da takeyi atimes yasa ya samo mata nutritionist me kula da cin abincin mara lafiya. Morning sickness kuwa bata dena ba har a yanzu dakuma kasala kamar yadda female Dr ta fad’a musu se ta wuce first trimester’n ta zata dawo old self nata. Sosai Anas yake kula da ita kusan a kullum sesun ma baby nasu shopping duk abinda Anas yagani ina a store kokuma online seya siya wa baby’n, bayi barin komai ya wucesa. Duk yadda Fannah zata iya bi dan hana Anas sanar dasu Mami da Ummie tana da ciki tabi amman haka seda ya kirasu ya fad’a musu tsantsan murna, duk suka tayasu murna babu kamar Afrah dake ma Fannah wak’a wai taci wake. Anas fa ba wasa tuni ya bada d’aki d’ayan dake tsakanin d’akinsa dana Fannah aka soma renovating dam aka cikasa da kayakin wasa da had’ad’d’un gadajen baby har guda biyu wanda yayi placing order daga Italy koda Fannah ta tambayesa dalilin dayasa akayi painting d’akin baby pink ce mata yayi wai ji yake ajikinsa mace kyakkyawa zata haifa masu me blue eyes kamar nasa danko har mafarki yayi, dad’i sosai taji, Anas is her everything bata tab’a neman abu k’ark’ashinsa ta rasa ba sesa a kullum take masa addu’a Allah ya cigaba da kare mata shi. A kullum kafin yadawo daga aiki suna kan video call inkuwa ya dawo suna a d’akin babynsu suna admiring d’akin, ga story books dam cike a cikin shelve d’akin baby on board na Mr. And Mrs. Fauzi kam se wanda yagani! 2 weeks after first visit nasu suka sake komawa asibiti akayi scanning cikin, baby’n na nan cikin k’oshin lafiya kuma sosai ya k’ara girma compared to zuwansu na farko, cikin nata nada 7 weeks yanzu sam kamar bame ciki ba, cikin nata na nan flat shide Anas ya k’osa yaga lokacin da cikin Fannah ze fito kodan yasamu abin neman tsokanarta. ★★★★★ _3 Weeks Later..._ Cikin Fannah nada 10 weeks cus! 2 months two weeks kenan dake takusan fita a first trimester nata yasa yanzu morning sickness d’in ya ragu compared to da a hankali take gaining back k’arfin jikinta unlike before da kullum take cikin bacci cikin nata wani haske da fresh ya k’ara mata sosai ga wani cikowan datake tayi daga sama har dan haka tasoma zama da hijabi agida wai kunyar Anas takeji se in an lura yanzu za’a iya ganewa tanada ciki danko ya b’ullo kai kad’an wanda in tasa tight kaya yana d’an nunawa. Yau ranar ta kasance Tuesday kamar yadda tasaba ada ta cigaba dayi yanzu dukda Anas ya hanata amman sam tak’i jinsa. 6:00AM ta tashi ta had’a musu breakfast sannan ta tada Anas yayi wanka seda ya gaishe da babynsu sannan ya gaishe da Fannah bayan sun k’are breakfast ta tayasa gama shiri tana cikin gyara masa necktie tayi noticing kallon ta da Anas yake danko ‘yar vest ce kad’ai jikinta. “Habeebi wai me haka? Kadena kallo na haka.” Tayi maganan a lokacinda ta sauk’e hannunta daga wuyansa bayan ta gama d’aure masa neck tie d’in ta juya masa baya nan tashiga nemo hijabinta daman tasan this is coming. Juyo da ita yayi tare da sauk’e hannayenta data azasu kan k’irjinta tana karewa. “Flower kin gani kuwa?” “Ga meh?” Ta tambayesa fuskarta ad’an tamk’e. “Kasakemin hannu.” “Bakiga...” Yakasa k’arisa maganan dan yadda k’irjin Fannah daya cike dam ke d’aukar masa hankali. Hannu tasa ta mari kansa a hankali “Habeebi kabar kallo na haka banaso.” D’an k’ara yasaki “awch! Flower tsaya kiga” hannunta yaja ya kaita gaban dressing mirror “kiga fa” yace da ita yi tayi kamar bata gane me yake nufi ba. “Mezan gani?” “Flower wai so kike kice bakiyi noticing ba?” “Noticing meneh? Nikam bye ga jakanka d’auka ka fice.” Murmushi sosai ya saki “kema kinyi noticing kenan.” “Eh mana nida jikina taya barinyi ba, Habeebi yayi muni ne?” Ta tambaya fuskarta kan wanda zeyi kuka. “Oh common Flower ko kad’an it actually fits you kin ma fi kyau haka.” “Habeebi are you sure?” Ta juyo gaban mirror tana kallon kanta. “Yes Flower I love you.” “I love you too Baby nace ko driver ka turomun se ya kaini asibitin kasan tace yau mukoma kuma kanada meeting.” “Flower kibari mana muje gobe.” “Habeebi yau fa tace karka damu I will be fine.” “I will cancel the meeting.” “Habeebi no need off you go.” “Flower are you sure?” “Eh mana zuwa asibiti ne kuma sabon abu? Zanje indawo fine and good in shaa Allah.” “Okay in driver yazo ki kirani ki sanardani in kuka isa asibitin nanma ki kirani sannan inya dawo dake nanma ki kirani ki fad’amin I can’t afford it in wani abu ya sameki ko baby’n mu Flower.” “Yes Sir zanyi as you say in shaa Allah ba abinda ze faru.” Kallon d’an k’aramin cikinta ya tsaya yi ganin tasa hannunta cikin rigar ya sasa murmusawa “kinga cikinki ya fara fitowa very soon ze zama k’ato irin na Nigerian police.” Bugi cike da shakwab’a ta kai masa a hannu “haba! Habeebi banaso in shaa Allah ciki na bareyi k’ato ba.” “Se yayi kijira nan da months kawai kiga wonders” “Habeebi manaaa!!!” ta hau bubbuga k’afa. “LOL Flower” ya matso da ita jikinsa “karki damu ko ya kike koya girman cikinki yake you are still the slim, elegant Fannah Aleeyu Fauzi that I know nothing will ever change kinji?” Kai ta gyad’a masa tana murmushi sanan tayi hugging nasa. Har bakin k’ofa ta rakasa as always ta miqa masa jakansa sannan tamasa goodluck kisses shikuma yayi kissing cikinta tare da cemasa ko ita “I love you” ganin Fannah ta had’a rai ya matso kunnenta itama yayi whispering “I love you also Baby Mamah” se anan ta murmusa “I love you too Habeebi, take care of yourself for me and our baby” “I will Flower and you too in na dawo se muyi maganan wani country kikeson muyi proceeding ante natal namu” zatayi magana ya dakatar da ita ta hanyan aza yatsansa kan bakinta “shhh! Flower na fad’a miki ni ba’a Nigeria nakeson ayi rainon babyn mu” tana murmusawa ta gyad’a masa nan ya fice da murmushi d’auke a fuskokinsu both seda gate ya ruhu ta dawo ciki. ****_10:30AM_ Dai-dai nan driver yazo d’aukan Fannah kamar yadda Anas ya buk’ace ta haka tayi dasuka isa asibitin ma ta kirasa again bayan angama dubanta driver yadawo da ita gida ko jakarta bata ajiye ba ta zaro wayarta ta danna masa kira bada jimawa ba ya d’aga. “Halo Habeebi” “Yes Flower... Har ya dawo dake gida ne?” “Eh yanzu shigowa na ko jaka ma ban ajiye ba nace barin kiraka.” “Thank you honey, so how is our baby?” “Its fine Dr tace in pregnancy’n yakai 4 month za’a iya gano sex d’in.” Cike da jin dad’i yace, “wow! Great news I can’t wait.” “Me either I have a suprise for you.” “Again? Flower bakiya gajiya da bani suprises and I love them.” “Saboda ina sonka Baby yau zan baka hint na suprise d’in.” “Really? Toh inaji” “Its regarding our baby.” “Ohh wow! What about it?” “Kai Habeebi kanamin wayo kanason in sanar dakai koh?” “Please Flower...” Yayi pleading. “Okay nasa anyi mana printing photo scan d’in.” “Haba! I can’t wait indawo gida.” “And guess what?” “What?!” Ya tambaya ba tare da b’ata lokaci ba. “Legs and hands na baby namu sun k’ara tsayi kuma har sun fara girmar da faracu.” “Dagaske Flower?!” Yayi exclaiming cike da jin dad’i. “Wallahi Habeebi its soo cute karka damu nayi printing out 3 pictures in kadawo zan nuna maka.” “Happy us Mammy and Daddy, kinsan wani abu?” “A’a Habeebi seka fad’a.” “In nadawo we will think of wani suna zamu bawa baby’nmu.” “Habeebi ai toh bamusan gender d’inba.” “Nifa na fad’a miki mace ce.” “Toh inkuma na miji ne fah?” “Se muyi suggesting 5 names na maza 5 names na mata ciki semu zab’a two dayafi dad’i na both sexes.” “Yeyy! to seka dawo I love you.” “I love you so much more Flower yanzu kije ki kwanta kihuta kinji?” “Yes Baby bye.” Nan tayi hanging hannu tasa zata zaro photo d’in dan sake gani aka danna door bell “wayene?” ta tambaya daga nesa. “D... Dr... Driver ne Hajiya.” “Moosa?” Ta tambaya tana nufowa bakin k’ofar. “Eh.. Ehh shine” yayi stammering again. “Toh meya faru haka?” Ta tambayi kanta ba tare da b’ata lokaci ba ta bud’e k’ofar ganin fuskarsa tayi duk jini ga idansa d’aya daya kumbura sakamakon bugin daya sha ga dukkan alamu. Hannu ta aza a bakinta tare da zaro idanunta waje “Ya Salam Moosa meya same ka haka? Innalillahi wa inna ilaihi r-” bata k’are salatin ba taga mutum from nowhere ya b’ullo a bayan Moosa rik’e da bingida a hannusa ya d’aga sama. Wani erin mumunan fad’i gabanta yayi wanda ta jima batayi erinsa ba da yazo da mumunar k’arshe da cikin dake jikinta ma seya zube take a wajen dan yadda ta tsorata, takuma tsure, zuciyarta se bugun d’ari-dar’i yake a yayinda bakinta ke b’ari ko kiran sunan mutumin ma takasa dukda kuwa bayau tasoma ganinsa ba... *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:58, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕, Ummee, Anee and Lilmeerahcute.* 7⃣9⃣ Alokaci guda k’wak’walwarta tabar aiki dan irin matsanancin tsoro da fargaban da ta shiga ji take inama ace mafarki ne. B’ari sosai both jikinta da bakinta suke “Fff.. Fa... Ya Farouq?” Ta kira sunansa cike da tashin hankali dakuma rashin yarda gashinan zahiri a gabanta amman jikinta yak’i yarda mata shid’in ne. Bakin bindiga ya sake bugawa kan Moosa seda ya fad’i sume a wajen. K’ara ta saki sosai tare da toshe kunnuwanta wani irin la’anannen murmushi ya saki yana nan kamar yadda yake ba abinda ya canza tattare dashi illa duhun daya k’ara. “Ohh what a sweet voice I’ve been missing ashe matan nawa barata manta da suna na.” Da k’afansa ya shure Moosa gefe guda dan wucewa ganin hankalin Fannah tashe akan sumemmiyar jikin Moosa yasa yace, “wifey karki damu dashi, kuma haka ake karb’an baqo ne? ba ko sannu dazuwa toh shigo da kaina inga wannan one in town mansion da ake ta maganansa a gari.” Nan ya miyar da bindigan aljihunsa yazo shiga kenan wani erin k’arfi yazo mata alokaci guda ta ture k’ofar sede aikin gama yariga ya gama hannu yasa ya kareta daga rufe k’ofar d sauri “wifey wai haka kike karb’an bak’i? oh please don’t be like this.” Baya baya ta soma yi har yanzu se b’ari take ganin haka ya cafko hannunta da k’arfin dayasa hawaye suka ciko mata a ido. “Ina zakije wifey?” “Yyy... Yya Farouq dan Allah ka sakemin hannu ba kyau ka sakeni please na rok’eka da Allan da rana ke hannunsa let me go...” Ta k’are maganan cikin sautin kuka. “Ohhh wifey don’t cry please kinji? Banason ganin hawayen nan” hanky yaciro na k’arfi da yaji ya share mata hawayen har a yanzu bata bar k’ok’arin k’watan hannunta ba. “What a wonderful house inhar Mr. Fauzi ne yayi desging to gaskia kudos to him gidanku yayi kyau sosai baraki d’an zagaya dani ciki ba nima in d’an gani wifey?” Ya k’are maganan dawani maqirin murmushin daya karkato ta gefe d’aya a fuskarsa. Hawaye take har a yanzu “Ya Farouq I’m not your wife kuma dan Allah kayi hak’uri ka koma inda kafito, ka sakemin hannu please matar aure ce ni ba kyau” ta sanar dashi cikin murya me rawa. “Ohh wonderful wifey ya kike magana haka? Rabuwa na dake tun yaushe amman ace wannan kalamu zaki fad’a mun don’t you miss me? Ko kad’an bakiyi missing d’ina ba?” Hannunta ya ja da k’arfi seda ta fad’a jikinsa. “I missed you wifey, kullum da tunaninki nake kwanciya in tashi inkuma sake yini dashi.” K’irjinsa take bubbugawa da k’arfin da Allah ya bata tana kuka tana had’asa da Allah amman ko a jikinsa se sake matseta yake yana shunshuna daddad’an k’amshin jikinta dukda haka bata bar kaimasa bugi ba seda yagaji ya raba jikinsa da nata hannunta still rik’e da nasa a hanakli ya murza hannun nata. “What a soft skin wifey, kinga wani fresh da kika k’ara kuwa? Mr. Fauzi ya riqe min amanar ki...” D’an hamma ya saki “yunwa nakeji nasan gidan Mr. Fauzi ba’a rasa kayan dad’i” hannunta yaja zuwa dining space ya bud’o fridge tare da ciro bufallo wings guda biyu da chapman drink, kan dining ya zauna ya buk’aceta da tayi hakan itama sam tak’i. Bindigan aljihun nasa ya ciro nanma tak’i se b’ari take duk yadda tayi dan kwantar da hankalinta ta kasa batason tsantsan tashin hankali tayi miscarrying babynsu, murmushi kad’an ya saki cike da mugunta “ko ki zauna kokuma in bindige kan Moosa dake waje.” “Ya Farouq mesa kake haka? When will you ever stop dan Allah? Me Moosa ya maka da zaka masa haka? Shin bakada imani ne?” “Imani? Yes Fannah banidashi sabida na siyar wa shed’an akanki Fannah kowa ze iya mutuwa bakisan yadda nakesonki bane shiyasa kike min wannan banzar maganar” rigan shirt nasa ya sauk’ar ya nuna mata tattoo dake hannunsa “ko ban fad’a ba kema kinsan hat F&F stands for, now sit!” Ya daka mata tsawa cike da tsoro ta zauna gefensa se hawaye take kamar lalacaccen famfo cikin kwanciyar hankali yagama cin abincinsa sannan ya kora da drink ko kubya babu. “Tunda kink’i zagaya dani I think its time to go” ya sanar da ita a lokacin daya mik’e yana k’ok’arin rik’o hanunta. Hannun nata taja ta sa cikin hijabi sannan ta hsare unstoppong hawayenta, “go where Ya Farouq? Where are you taking me? Dan girman Allah karka min haka ka tausaya min please.” “Wifey ai tausayin ne yajawo haka” cike da mugunta ya miqar da ita daga saman hannunta wani irin wahalallen k’ara ta saki “Anas! Anas! Anas! dan Allah kazo ka taimakeni, Anas pleaze come.” ta fashe da kuka... “Chill chill wifey Anas naki ba yanzu zezo ba saboda yana da meeting 1:30PM to 2:30Pm so kinga se k’arfe uku ko hud’u kamar yadda ya saba ze dawo dan haka kima bar kiransa for help.” “Ya Farouq me kakeso wallahi in kud’i ne zan baka dayawa muje safe na Anas zan baka ko nawa kakeso amman dan Allah karka kaini wani wajan karka rabani da gidana da mijina please Ya Farouq ka tausaya min nasan I can’t fight you kaji k’aina please.” Ta k’are maganan tana kuka sharqaf sharqaf. “Ohh wifey meyayi zafi haka? Bar kukan nan please zancen kud’i kuwa wanda kike kira da mijinki shi ze dank’a min arzikinsa gabad’ai yanzu lets go.” Bata bar rok’ansa ba har a yanzu se janta yake da k’arfi tana jan kanta baya tana ihu tana kiran sunan Anas har sun kai da bakin k’ofa ya dakata yaje ya d’ago jakarta da wayanta sannan yasa hannu a aljihunsa ya ciro wani ninkekken takarda ya ajiye gab da bakin k’ofar sa’annan ya bud’e k’ofar har a yanzu Moosa na nan a sume k’ara k’arfin sautin kukanta tayi tana me kiran sunan Anas har a yanzu. Cikin motan da driver ya turo Anas k’irar Audi jeep 2016 yasata ciki tare da zaro handcuff ya had’e hannunta da k’ofar ta yadda barata iya guduwa ba sannan yaje yaja sumemmiyar jikin Moosa yakai gefe d’aya daga cikin motocin da akayi parking nasu a lot kome ya sake canza masa ra’ayi se kuma ya sake jan Moosa yakai motar dayakeson tafiya da Fannah, cikin open booth ya jefa Moosa. ***** Anas na zaune a office nasa dawasu files na Unity Global intercome yana going through kawai seyaji gabansa yayi wani irin mumunar fad’i wanda ya rasa dalilin hakan, coffeensa da Fannah ta had’a mai ya zuba kad’an a cup yasha amman inaaa yakasa samun sukuni rolex agogon hannunsa ya duba yaga 12:32PM har ya d’ago wayarsa dan kiran Fannah kuma se ya tuna ashe d’azu ya buk’ace ta takwanta tayi bacci bari ya tura mata text message kar ya tak’ura mata. Da murmushi a fuskarsa yamiyar da wayan bayan yayi mata sending ya ajiye sannan ya cigaba da abinda ke gabansa... *ANAS* _3:57PM_ Shigowan Anas gida kenan bayan ya miyar da k’ofan ya juya yana neman Flowersa normally inba wai bacci take ba she’s always around tamishi sannu da zuwa sab’anin haka yayi concluding a ransa koda bacci take har yanzu. D’akinsu ya nufa to his suprise be ganta ciki seyayi tunanin ko tana bayi, dining ya dosa dan ciro bufallo wings daya siyo wa kansa dankuwa Fannah bata ci sama da k’asa ya nema abinsa ya rasa mamaki ne kwance a fuskarsa. Yaushe Fannah ta iya chin bufallo wings da har zata cinye guda biyu? “Wow!” Yayi exclaiming a fili “bade cikin naki ze miyar dake glutton ba Flower.” Packaged chicken yaciro yad’an ci kad’an dan bawani yunwa yakeji ba bayan ya k’are ya koma d’aki sede still ba Flowersa bayin ya dosa yayi knocking. “Flower?” Ya kira sunanta. “Flower kina ciki ne?” Jin shirun yayi yawa ya murd’a hannun k’ofar ya shiga sede ba Flowersa ciki anan fa hankalin Anas ya fara tashi, d’akinta ya dosa a gurguje nanma ba ita ba alamunta haka ya duba d’akin babynsu nanma ba Fannah tirk’ashi! Gidan kap ya zagaye yana kiran sunanta yana nemanta aman ba ita ba alamunta ba. Toh kode tafita ne? Ina ma zataje ai Flower bata zuwa ko ina kuma inda wani gun zataje da ta sanar dani, toh ina take? A rashin samun amsoshi ga wad’annan tambayoyin yasa ya koma ciki dan d’auko wayarsa ya kirata yaji daga bakinta yashiga kenan kasancewar ba takalmi k’afansa yaji kamar ya taka abu a nitse ya miyar da kallonsa kan right foot nasa inda yakejin ya taka abu bayan ya matsar da k’afan yaga paper ne aninke dudum! Yaji zuciyarsa ya sake bugawa fiye da na da se ayanzu yakejin something bad is happening to his Flower and baby ba tare da b’ata lokaci ba ya d’ago paper’n ya bud’e cikin sauri ya soma karantawa; _Welcome back home Mr. Fauzi gida yayi kyau masha Allah nagode da riqe min amanan *whats mine* da kayi. I know baka mance ba whats mine is MINE 09011140607 you might get the chance to listen to her voice if you are lucky. Team F&F_ Rawa jikinsa ya soma a yayinda tunaninsa ya jaqule, wani irin gumin da ko ACn ma yakasa d’aukewa ne suka soma gangaro masa from nowhere, blue eyes nasa suka sake shiga darker tsabagen tashin hankali, migraine nasa ne ya bugo sa a lokaci guda wanda bare iya tuna when last rabuwarsa dashi ba. Hannu yasa ya dafe kan nasa cike da azaba ayayinda k’afafunsa ke rawa. “FAROUQ!” ya furta a hankali cike da tashin hankali. ***** *FANNAH* _Chan bayan garin Maiduguri_ Cikin wani abandoned uncompleted building me steps kusan biyar wanda ba’ayi painting ba windows ma ba’a gama sawa ba a floor na k’arshen. Irin tsagerun unguwa masu shaye shaye ne guda biyar k’ati a bakin entrance door d’in da alama gadi suke. Cikin gidan a second floor cikin wani d’an madaidaicin d’aki wanda yake nan da k’aramin rug seda sofas guda biyu da k’aramar fridge seda gado cikinsa. Fannah ne ke zaune kan wani kujeran katako hannunta da k’afafunfa duka d’aure jikin kujerar bakinta kuwa makeken cellotape ne anrufesa dashi hawaye ne ke gangarowa har yanzu kan lallausar kumatunta. Fuskar nan nata yayi ja dan kuka nishi take a hankali abin tausayi ayayinda Farouq ke tsaye a kanta yana shafa sajen fuskarta dayasamu fitowa dan yadda hijabin jikinta yayi baya. “Wifey I told you to stop fighting amman kink’i inda kin bani had’in kai daduk hakan be faru ba, bakiga d’akin dana gyara mana bane dake 3rd floor? Just for me and you nasan kin saba da california bed agidanki but karki damu jiran call nake daga gun Anas yana turomin kud’i zan canza mana gida sorry you have to manage.” Y’unkurin magana take amman ba hali dan cellotape dake bakinta. “Shhh! Ba sekinyi magana ba so kike na cire miki wannan?” Yashafa kan celotape d’in ta inda bakinta yake. Kai ta kawar da wuri idanunta basu bar tsiyayar hawaye ba har a yanzu. ‘Yar murmushi ya saki “ya naga kamar kina zufa? Acire miki hijabin ne?” Yana tab’ata tahau shure shure da d’an k’arfin daya rage mata a jiki. “Kunyar nan taki ta munafirci na nan LOL karki damu zan cire miki shi a first night namu” dawo da kallonta tayi garesa tare da watsa masa wani irin disgusting kallo a zuciyarta tana me tsine masa albarka. “Sweetheart don’t look at me your husband like that banson raini.” Jakarta dake kan medim sized bed ya d’ago tare da zazzagewa. Kud’i ne almost a bundle na d’ari biyar ciki seda turaruka da d’an kayan kwad’ayi irinsu tuwon madara, tsami gaye, tsamiyan biri da sauran tarukuce sam hankalinsa bekai kan photo scan dake a gefe ba. Kud’in ya d’aga yasa a aljihunsa duka sannan ya d’ago wayarta ganin new message from Habeebi yasa yad’an murmusa “wifey bari muga wani saqo Anas ya turo mana” nan ya shiga ya karance a fili kamar haka; _How lucky I am. I am falling and falling deeply in love with_ _the prettiest girl in the world. I am not ashamed to say this. Infact, I am proud of you and I'm not going to let you go, remember those times when I woke up in the middle of_ _the night just to watch your innocent face while you sleep? Remember those times when I woke up very early in the morning just to to serve you coffee in bed?_ _Remember_ _those times when I hold your hands tight and find it difficult to let you go? It’s because I love you so, and I long to be with you more. This is no mere words, it's_ _from the depths_ _of my heart. I love you Flower._ Dariya sosai ya b’arke da “stupid kawai† yafad’a a fili. Nan k’arfin kukan Fannah ya dad’u kuka take sosai abin tausayi a yayinda son Habeebinta ke sake shiganta da zafi da zafi. “Ignore the bastard wifey” nan yayi deleting message d’inma kwata kwata tare da ajiye wayan a gefe sannan ya hau tattara tarukucan su tsamiyan biri gefe guda. “Wifey bansan ki da ciye ciye haka bafa, taya Mr. Fauzi ze barmin ke kina wannan ciye ciyen k’aza-” be k’are maganar ba idansa yakai kan d’aya daga cikin photo scan d’in, sam begane me aciki ba seda ya d’ago ya matso dashi kusa da idanunsa yana examining anan ne ya gano kan mutum ne ga kuma hannaye da k’afafu dara-daran idanunsa ya zaro waje disbelievingly kai ya soma kad’awa gudun kar abinda zuciyarsa ke sak’a masa yazamo gaskia cike da tashin hankali ya maido da kallonsa kan crying Fannah wani irin tafasa zuciyarsa ke ga kishi bayyane karara a fuskarsa tun ba yau ba abinda yake gudu kenan rananda Fannah zata d’au cikin wani ba nasa ba. “Ke!” Ya danna mata kira cikin wani irin husky voice sosai ta tsorata amman tak’i koda d’ago kai ta kallesa. A fusace ya mik’e ya nufo gabanta tare da murd’a mata kai seda ta kallesa na dole “meh wannan?” ya d’ago hoton yana nuna mata. Bayan data kalli hoton sekuma ta sake fashewa da kuka babban tashin hankalin da take ta guduansa kenan, tun d’azu addu’a take kar Allah yakai Farouq jakarta tsoronta shine karyace ze illata mata baby she can’t afford to lose her baby ya mata komai amman karya tab’a mata baby. “Magana nake miki ba kuka nace kiyi ba. What is this?” Tsantsan kishi yariga ya mamaye masa zuciya besan a lokacinda ya d’aga hannu yakai mata wawan mari a fuska ba dukda bakinta a rufe ne amman seda d’an k’ara ya fito a yayinda hawaye ke ambaliya kan fuskarta. “Meh wannan nace? Ciki kike dashi? Ciki?! Waya miki cikin? Am talking to you! Anas koh? Hahaha...” ya sakar da wata muguwar dariyan bosawa. “Bazata saku ba, Fannah you are mine baraki d’au cikin wani mahaluqi ba a duniyan nan ba se nawa muddin ina raye. Ki ware kunnuwanki da kyau ki saurare ni” ya nunata da yatsa “zubar da wannan shegen cikin Mr. Fauzin zanyi in kinga kin haihu da d’an wani toh Farouq ya mutu baya duniya” shaking kujerar take tana kad’a masa kai tana hawaye sosai aranta kuwa ba abinda take se kwararo addu’a... *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:58, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 8⃣0⃣ Daidai yakai da bakin k’ofa ya murd’a handle d’in a fusace kenan wayarsa dake aljihunsa yasoma ringing dogon tsuka yaja sannan yaciro wayar ganin new number yasan Anas ne dan kuwa beyi registering numban kowa kan sim d’inba. Wani shu’umin murmushi ya saki sannan ya maida hannun k’ofar ya dawo ciki tare da zama kusa da Fannah. “We are having a call from Anas wifey.” yasake murmusawa. Ba tare da b’ata lokaci ba ya d’aga tare da sawa a handsfree yana shafa hannun Fannah a hankali in a romantic manner se k’ok’arin shuresa take amman takasa. “Halo Farouq?” cewar Anas. D’an dariya ya saki “huh! How smart you are Mr. Fauzi harka gano nine na ma wannan big suprise d’in kenan? Well bravo.” “Shut up you bastard where is my wife? Ina ka kaimin matata?” “You shut up Idiot ko kayi behaving kanka kokuwa har abada baraka sake sa Fannah a idanka ba, mschw!” “What do you mean Farouq let her go ka saketa dani kake da problem ba Fannah ba niya kamata ka kama ba ita ba, why are you such a coward?” “Coward? Dan na karb’o whats mine shine zaka cemin coward?” “Fannah was never yours and never will be-” katse sa yayi “don’t you dare Anas karka sake katseni idan ina magana yanzu ba wannan ba idan kanason sake jin voice na Flowerka you do as I say.” “Farouq don’t dare touch her karka kuskura ka tab’a Fannah wallahi I will kill you inhar wani abu ya sameta.” “LOL” ya k’yalk’yale da dariya “kill me? Ashe I will dye along with your Flower saboda nikeda iko da ranta yanzu aduk lokacin dana ga dama ina iya kasheta inkazo nima seka kasheni kaga ko semuje mucigaba da soyayyar mu kamar yadda muka saba chan a lahira kaikuma a barka anan.” “Farouq you are going straight to hell and don’t you dare touch her-” “Then behave yourself” ya katsesa. “Naji I will karka tab’ata please.” “Hohoho did the mighty Mr. Fauzi just said please? Lallai fa kanason Flower nan taka sede ba kamar yadda nakeson taba.” “Farouq please shut up kafad’amin inda take banida lokacin jin nonsense naka, ina ka kaimin mata?” “In fad’a maka inda take? Karka damu very soon zaka sani sede you’ll pay an amount in return. Kuma the next time ka sake cemin nonsense ka yarda dani baraka sake sa Flowerka a ido ba” ya k’are maganan yana shafa fuskar Fannah. “Me kake nufi Farouq? Ransom?” “Brilliant sesa nakeson harka da mutane masu ilimi kamarku ransom nake nufi” “Farouq kasan meh? You are going straight to hell.” “And your Flower is going with me” nan ya d’aga hannu yasake shafo fuskar Fannah da sauri ta kawar da kanta. “Ina take yanzu? Taya ma zanyi trusting maqaryaci kaman ka? Taya zan yarda Fannah *_TANA TARE DA KAI?”_* “Smart guy barin maka proving” cike da mugunta yasa hannu ya b’antare cellotape dake bakin Fannah wani irin azabartaccen ihu ta sakar wanda Anas yaji har tsakar kansa sannan kuma ta rushe da wani erin wahalallen ihu. Cike da tashin hankali Anas yayi maganar. “Flower! Flower!... Farouq please karka tab’a ta I will do anything dan Allah nace don’t touch her please...” “Shhh!” Yace da Fannah yana shafa bayanta har a yanzu bata bar kukan ba, nan ya dawo kan wayar. “Mekace Mr. Fauzi?” “Anything Farouq please karka tab’ata I will do anything ka had’ani da ita please.” “Zan had’aku na minti d’aya in exchange of N500,000 (dubu d’ari biyar) inkuma kanason kaji muryar Flowerka fiye da minti d’aya sekayi multiplying kud’in per minute N500,000 and karka yimin wasa da hankali zan maka sendn bank details d’ina inhar banga alert ba zuwa yamma believe me baraka sake sa Fannah a ido ba.” “Farouq are you crazy? Wani irin hauka ne haka?” “Fine and good bakason jin muryarta kenan am hanging up” fuskar Fannah ya juya cike da muguntan da yasata sakar da k’ara. “Please don’t okay, okay I will ko nawa kakeso zan baka please kadena sata kuka.” “Good boy Anas ga Flower ku gaisa kunada minti biyu” nan yasawa Fannah wayar a kunne cikin sautin kuka ta kira sunansa “Habeebi” “Shhh! Flower don’t cry kinji?” magana take cike da tashin hankali dakuma tsoro. “Habeebi ina tsoro dan Allah stop him yace ze zubar min da ciki, Habeebi ze kashe mana baby, dan Allah ka barsa ka hanasa karka barsa please Hab-” bata k’are maganar ba Farouq ya ciro wayar daga kunnenta “munafirci kike agabana?” Nan ya mik’e “kuma cikin seya zube, sena zubar kina wasa da Farouq.” fashewa tayi dawani erin matsanancin kuka jin haka Anas ya sake kid’imewa “Hello...?” Anas yayi maganar cike da tashin hankali. “Hello Farouq please speak up.” “Meh? Meh? Kana cika min kunne fah.” Cewar Farouq ganin Fannah nada niyyan sake magana yayi sauri ya toshe mata baki da hannunsa d’aya. “Farouq dan Allah kabar sata kuka, karka tab’a lafiyar Fannah I beg you ko nawa kakeso zan baka dan Allah karka mata wani abu she is sick already please karka mata wani abu.” “Hohoho!!! Mr. Fauzi ashe ka iya rok’an mutum sede kash! Barin bar shegen ajiyar da kayi cikinta yaje ko inaba I must destroy it” jin haka Fannah tacize masa hannu da k’arfin da Allah ya bata take ya jefar da wayar wanda beyi landing ko ina ba sekan cinyan Fannah. K’ara sosai ya saki se buga hannun nasa yake a iska cike da azaba. Anan tasamu daman magana “Anas Habeebi please help me dan Allah karka bari yamin wani abu Anas our baby please stop him.” “Shhh! Flower bar kuka kinji its bad for your condition kuma in shaa Allah ba abinda ze miki. I won’t rest sena k’wato ki hannun Farouq bar kuka. Kinsan ina ya kaiki? Kinsan address d’in wajen?” “Habeebi bansani ba a sume ya taho dani gidan all I know is babban buildin-” bata samu daman k’are maganar ba sakamakon marin da Farouq ya wanketa dashi wanda har cikin kunnen Anas seda yajiyo k’aran marin kuka tasoma papawa ba makawa abin tausayi. “Ni zaki ciza? Eh? Bakida hankali ne?! Karki damu by the time na zubar da shegen abinda ke cikinki zaki shiga hankalinki mschw!” ya sake kallon hannun nasa a fusace sannan ya katse wayar tare da cire sim d’in ya taune sannan ya yasar. Kuka sosai Fannah ke kamar zata cire ranta. Wayanta dake kan gado ne ya soma ringing Farouq na dubawa yaga Habeebi wani dogon tsuka yaja sannan ya katse wayar nan Anas ya sake bugawa Farouq na katsewa kusan sau uku se a karo na haud’u Farouq ya d’aga. Cike da tashin hankali Anas ke maganar “Farouq please karka ma Fannah wani abu, karka rabata da babynta ko nawa kakeso zan baka please don’t do such evil please karka rabata da abinda ke cikinta ka fad’a ko nawa kakeso zan baka please Farouq...” “Huh! Let me see yanzu senayi tunani, zaman da zanyi dan gudanar da tunanin is 2 million sannan inna yanke hukunci sanar dakai zanyi nanma 2 million, kanaji na?” “Inaji Farouq wannan ba matsala bane please karka mata wani abu batada lafiya she is your sister please karka mata wani abu.” “Naji seka fad’a mata karta min misbehaving if not I might lose my patience.” “Okay zan mata ka bata wayar please.” “Kasani each minutes costs N500,000 d’azu kunyi 2 minutes 1 mil kenan.” “Farouq yaushe mukayi 2 minutes ba katse wayar kayi ba?” “Then fine zan kashe wayar-” da wuri Anas ya katse sa, “A’a please kar ka katse I will pay just give her the phone.” “Good” nan ya maido da kallonsa kanta “ke! Gashi sauran kimasa wani munafircin kiga in ban rabaki da shegen dake cikin ki ba.” Hannu d’aya ya since mata tare da bata wayan sannan ya yi gefe guda a d’akin yana me zuba mata ido. “Flower kinaji na?” cewar Anas. Cikin sautin kuka ta amsa “eh Habeebi.” “Good kibar kuka kinji? And kiyi duk wani abinda ya buk’ace ki muddin be sab’awa muslinchi ba I promise I will let yo out of there, I love you.” “Habeebi I miss you please karka d’au lokaci kazo ka d’aukeni, I don’t trust Ya Farouq dan Allah Habeebi.” “Flower stop panicking and do as he says I will come in shaa Allah kinji? Kibar kuka zeyi affecting lafiyarki, I love you.” “I love you too Habeebi, I love you so much.” Kafin Anas yasake cewa wani abu Farouq ya fisge wayan “time up!” ya sanar da Anas. “Farouq please ka bata wayan I will pay you.” “Nasani sede kakai limit naka na yau sekuma gobe if you are lucky.” “Please Farouq.” “Why being so insistant? Wallahi ka sake roqana baraka sake magana da ita ba mschw!!” “Okay but please Farouq feed her kabata abinci kasan condition nata zama da yunwa won’t help.” Kallon faracunsa yake sannan yace, “aww! kana nufin wai shegen cikin dake jikinta?” “Eh shi Farouq dan Allah feed her karka barta da yunwa.” “Toh ai banida kud’in bata kalan abincin data saba ci a gidanka ka turo kud’i kamar miliyan d’aya haka se a siya mata abinci me kyau.” “Okay I will do it, zanyi just kar ka barta da yunwa.” “Naji kana cika min kunne zan maka sending acct details d’ina sauran ka b’ata a irgen kud’ina kaga tashin hankali” yana kaiwa nan ya katse wayar nan da nan yatura wa Anas acct details nasa ba tare da b’ata lokaci ba Anas yama PA’nsa magana akayi ma Farouq transfering 7 million yana zaune a gefen Fannah yana gasa mata bak’ak’en kalamu alert yashigo ta wayarsa bayan ya duba ya sakar dawani shu’umin murmushi “wifey mijin nakin nan baya wasa now you can have your lunch tunda ya cika alk’awari” wani number yayi dialing a wayarsa; “Okay angama had’a dining d’in?” “Eh Boss angama komai is ready.” “Good!” nan ya katse. Igiyoyin da yabi ya k’ulle mata jiki dasu yabi ya sissince “tashi muje kichi abinci wifey.” K’in miqewa tayi cike da mugunta ya miqar da ita daga saman hannunta k’ara soai ta sakar haka ba tausayi yajata zuwa wani had’ad’d’en d’akin da aka tsara sa as dining room dogon table ne wanda aka cika sa dam da abinci kala kala wane (feast) kujeru biyu ne kad’ai a both ends na table d’in kujera d’aya yaja mata ya zaunar da ita sannan yakoma nasa shima ya zauna. “Eat my lady duka wannan naki ne kichi babynki yasamu yaci shima kafin in rabaki dashi.” “Ya Farouq mesa kake haka? Me na maka? Yanzu zakaso ache kanada sister sannan wani yana mata haka?” Fork yakai baki “unfortunately banida sister so kichi abinci.” “Kabani dalili d’ayan da zesa inchi wannan abincin, nasani ko kasa abinda ze zubar min da ciki aciki, banaso.” “Wifey kinga karki min rashin kunya anan eat.” “Barin chiba Ya Farouq dan Allah ka fitar dani daga nan ka kaini gida gun mijina please.” Banza da ita yayi ya d’au wayarta ya kira Anas ringing d’aya Anas ya d’ga “hello.” “Mr. Fauzi” “Na’am Farouq baka ga alert d’in bane?” “Nagani kama Fannah magana tadena cika min kunne da surutu I might lose my patience and if that happens zaku iya rasa shegen ku.” “Kabata wayar please I will talk to her.” “Na fad’a maka ka riga kayi exhausting time naku na yau.” “Nasani Farouq ka taimaka please.” Ido yama mutumin dake gefensan tare da miqa masa wayan yakai wa Fannah. “Hello Flower please kichi abincin kinji? Ko kinason abu ya samu babynmu?” Kai ta kad’a wane yana kallonta. “Kinaso?” “A’a banaso Habeebi bansani ba koyayi poisoning abincin.” “Beyi ba Flower in shaa Allah beyi ba kichi kinji? I’m coming for you I love you.” Bata samu tace masa she loves him too ba mutumin ya k’wace wayan. Plate d’in ta jawo tayi bismillah sannan takai kad’an daga cikin pepper soup d’in kifin bakinta a hankali tasamu tad’an cika cikinta fargaba ya hanata k’oshiwa. Bayan sun gama ya buk’ace ta data bi bayansa. “Ya Farouq kai baka Sallah ne? Dukda bansan k’arfe nawa bane amman nasan Azahar da La’asar sun wuceni.” “Ohh wifey ni ai banayi had’asu nake duka se isha zan yi amman tunda kince haka taho in rakaki” bejira tace komai ba yaja hannunta zuwa d’akinsu daya tanar masu har cikin bayin ya rakata “ko kinason kiyi wanka?” “I wouldn’t mind tunda ba a cikin k’azanta ka d’aukoni ba” tabasa amsa tana me k’arewa bayin kallo mamaki ne yacika ta shin ina Farouq yasamu kud’i haka? Daya karanchi hakan seya murmusa “mamaki kike? Karki damu ba sata nayi ba bashi na karb’a kuma har na miyar musu da kud’in da Anas yaturon” sede har a yanzu bata bar kallonsa ba nufin bata da yarda ba. “Wallahi kuwa wifey ko mamakin ya akayi nasan gidanku kike? LOL long story;” _“Da barina prison yanzu sati biyu kenan bashin danaci na yi mana wannan siyayyan shine wanda Baba yayi amfani dashi yayi bailing d’ina kuma drugs ne source na kud’in. Inada wani abokin dake siyar da coccaine shine yabani bashin miliyan 5 dashi na aiwatar da komai. Bayan fitowana da kwana biyu na shirya tsaf naje Enterprise na Habeebinki namusu k’arya cewa business man ne ni ina kuma neman appointment dashi sam receptionist d’in ta hanani ganinsa saboda nak’i bata personal information akaina, me gadin wajen nasamu na tsara sa har seda ya fad’amin k’arfe nawa Anas yake tashi daga office anan ne nasamu nayi timing nasa bayan da aka tashi na biyosa anan ne na ga gidanku. Dalilin dayasa nasan rana kinfita kuma bada Anas ba kuwa itace yawan zama dana keyi a unguwanku ganin driver yazo ya d’aukanku naje na shirya nima, dawowa na yayi daidai da shigowarku achan na tsare driver bayan ya ajiyeki namasa tsinannen duka dan k’in bani had’in kai dayayi, seda nayi pulling masa bindiga ya yarda yakaini ciki. Dana jima da kashesa sede kuma naji anacewa security doors ne a gidan naku inba wanda yasani ba baya bud’uwa._ Any question wifey?” Kai kawai take kad’awa tana tausayawa d’an uwan nata kalan rayuwar daya d’au ma kansa. “Allah shiryeka Ya Farouq inhar kaid’in me shiryuwa ne shikuma Moosa daka rufesa a d’aki so kake ya mutu ne? Ka tuna d’an Adam ne shima mejin yunwa.” “Karki damu wifey your wish is my command yanzu yi wanka abinki cikin wardrobe akwai kaya seki zab’a d’aya ciki kisa, I love you.” Tsuka taja “wifey I said I love you.” “I hate you Ya Farouq na tsaneka.” Bakinta ya maquro “what did you say?” “I said I hate you, ka sakemin fuska mugu kawai” tahau kai masa bugi. “Quit it!” Ya daka mata tsawa. “Kin d’au wasa nake ko?” Hannu yasa ya yage mata hijabi tun daga sama har k’asa kafin ta hankara ya had’a ta da bango tare da kai hancinsa wuyanta yana wani shunshuna mata jiki. Hannayenta daya matse jikin bangon take ta k’ok’arin k’watansu amman takasa. “Ya Farouq dan Allah kabari” ganin yasoma wuce gona da iri ta qurma wani irin ihu dukda haka be dena gudanar da abinda yayi niyyah ba dabara ce ta fad’o mata k’afanta ta d’aga ta saita daidai abinsa takai masa bugi da k’arfi wani erin k’ara ya saki cike da azaba take a wajen ya durk’ushe anan ne tasamu ta k’wata kanta tare da d’ago hijabinta tana kare k’irjinta dashi. *© MIEMIBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:58, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 8⃣0⃣ Daidai yakai da bakin k’ofa ya murd’a handle d’in a fusace kenan wayarsa dake aljihunsa yasoma ringing dogon tsuka yaja sannan yaciro wayar ganin new number yasan Anas ne dan kuwa beyi registering numban kowa kan sim d’inba. Wani shu’umin murmushi ya saki sannan ya maida hannun k’ofar ya dawo ciki tare da zama kusa da Fannah. “We are having a call from Anas wifey.” yasake murmusawa. Ba tare da b’ata lokaci ba ya d’aga tare da sawa a handsfree yana shafa hannun Fannah a hankali in a romantic manner se k’ok’arin shuresa take amman takasa. “Halo Farouq?” cewar Anas. D’an dariya ya saki “huh! How smart you are Mr. Fauzi harka gano nine na ma wannan big suprise d’in kenan? Well bravo.” “Shut up you bastard where is my wife? Ina ka kaimin matata?” “You shut up Idiot ko kayi behaving kanka kokuwa har abada baraka sake sa Fannah a idanka ba, mschw!” “What do you mean Farouq let her go ka saketa dani kake da problem ba Fannah ba niya kamata ka kama ba ita ba, why are you such a coward?” “Coward? Dan na karb’o whats mine shine zaka cemin coward?” “Fannah was never yours and never will be-” katse sa yayi “don’t you dare Anas karka sake katseni idan ina magana yanzu ba wannan ba idan kanason sake jin voice na Flowerka you do as I say.” “Farouq don’t dare touch her karka kuskura ka tab’a Fannah wallahi I will kill you inhar wani abu ya sameta.” “LOL” ya k’yalk’yale da dariya “kill me? Ashe I will dye along with your Flower saboda nikeda iko da ranta yanzu aduk lokacin dana ga dama ina iya kasheta inkazo nima seka kasheni kaga ko semuje mucigaba da soyayyar mu kamar yadda muka saba chan a lahira kaikuma a barka anan.” “Farouq you are going straight to hell and don’t you dare touch her-” “Then behave yourself” ya katsesa. “Naji I will karka tab’ata please.” “Hohoho did the mighty Mr. Fauzi just said please? Lallai fa kanason Flower nan taka sede ba kamar yadda nakeson taba.” “Farouq please shut up kafad’amin inda take banida lokacin jin nonsense naka, ina ka kaimin mata?” “In fad’a maka inda take? Karka damu very soon zaka sani sede you’ll pay an amount in return. Kuma the next time ka sake cemin nonsense ka yarda dani baraka sake sa Flowerka a ido ba” ya k’are maganan yana shafa fuskar Fannah. “Me kake nufi Farouq? Ransom?” “Brilliant sesa nakeson harka da mutane masu ilimi kamarku ransom nake nufi” “Farouq kasan meh? You are going straight to hell.” “And your Flower is going with me” nan ya d’aga hannu yasake shafo fuskar Fannah da sauri ta kawar da kanta. “Ina take yanzu? Taya ma zanyi trusting maqaryaci kaman ka? Taya zan yarda Fannah *_TANA TARE DA KAI?”_* “Smart guy barin maka proving” cike da mugunta yasa hannu ya b’antare cellotape dake bakin Fannah wani irin azabartaccen ihu ta sakar wanda Anas yaji har tsakar kansa sannan kuma ta rushe da wani erin wahalallen ihu. Cike da tashin hankali Anas yayi maganar. “Flower! Flower!... Farouq please karka tab’a ta I will do anything dan Allah nace don’t touch her please...” “Shhh!” Yace da Fannah yana shafa bayanta har a yanzu bata bar kukan ba, nan ya dawo kan wayar. “Mekace Mr. Fauzi?” “Anything Farouq please karka tab’ata I will do anything ka had’ani da ita please.” “Zan had’aku na minti d’aya in exchange of N500,000 (dubu d’ari biyar) inkuma kanason kaji muryar Flowerka fiye da minti d’aya sekayi multiplying kud’in per minute N500,000 and karka yimin wasa da hankali zan maka sendn bank details d’ina inhar banga alert ba zuwa yamma believe me baraka sake sa Fannah a ido ba.” “Farouq are you crazy? Wani irin hauka ne haka?” “Fine and good bakason jin muryarta kenan am hanging up” fuskar Fannah ya juya cike da muguntan da yasata sakar da k’ara. “Please don’t okay, okay I will ko nawa kakeso zan baka please kadena sata kuka.” “Good boy Anas ga Flower ku gaisa kunada minti biyu” nan yasawa Fannah wayar a kunne cikin sautin kuka ta kira sunansa “Habeebi” “Shhh! Flower don’t cry kinji?” magana take cike da tashin hankali dakuma tsoro. “Habeebi ina tsoro dan Allah stop him yace ze zubar min da ciki, Habeebi ze kashe mana baby, dan Allah ka barsa ka hanasa karka barsa please Hab-” bata k’are maganar ba Farouq ya ciro wayar daga kunnenta “munafirci kike agabana?” Nan ya mik’e “kuma cikin seya zube, sena zubar kina wasa da Farouq.” fashewa tayi dawani erin matsanancin kuka jin haka Anas ya sake kid’imewa “Hello...?” Anas yayi maganar cike da tashin hankali. “Hello Farouq please speak up.” “Meh? Meh? Kana cika min kunne fah.” Cewar Farouq ganin Fannah nada niyyan sake magana yayi sauri ya toshe mata baki da hannunsa d’aya. “Farouq dan Allah kabar sata kuka, karka tab’a lafiyar Fannah I beg you ko nawa kakeso zan baka dan Allah karka mata wani abu she is sick already please karka mata wani abu.” “Hohoho!!! Mr. Fauzi ashe ka iya rok’an mutum sede kash! Barin bar shegen ajiyar da kayi cikinta yaje ko inaba I must destroy it” jin haka Fannah tacize masa hannu da k’arfin da Allah ya bata take ya jefar da wayar wanda beyi landing ko ina ba sekan cinyan Fannah. K’ara sosai ya saki se buga hannun nasa yake a iska cike da azaba. Anan tasamu daman magana “Anas Habeebi please help me dan Allah karka bari yamin wani abu Anas our baby please stop him.” “Shhh! Flower bar kuka kinji its bad for your condition kuma in shaa Allah ba abinda ze miki. I won’t rest sena k’wato ki hannun Farouq bar kuka. Kinsan ina ya kaiki? Kinsan address d’in wajen?” “Habeebi bansani ba a sume ya taho dani gidan all I know is babban buildin-” bata samu daman k’are maganar ba sakamakon marin da Farouq ya wanketa dashi wanda har cikin kunnen Anas seda yajiyo k’aran marin kuka tasoma papawa ba makawa abin tausayi. “Ni zaki ciza? Eh? Bakida hankali ne?! Karki damu by the time na zubar da shegen abinda ke cikinki zaki shiga hankalinki mschw!” ya sake kallon hannun nasa a fusace sannan ya katse wayar tare da cire sim d’in ya taune sannan ya yasar. Kuka sosai Fannah ke kamar zata cire ranta. Wayanta dake kan gado ne ya soma ringing Farouq na dubawa yaga Habeebi wani dogon tsuka yaja sannan ya katse wayar nan Anas ya sake bugawa Farouq na katsewa kusan sau uku se a karo na haud’u Farouq ya d’aga. Cike da tashin hankali Anas ke maganar “Farouq please karka ma Fannah wani abu, karka rabata da babynta ko nawa kakeso zan baka please don’t do such evil please karka rabata da abinda ke cikinta ka fad’a ko nawa kakeso zan baka please Farouq...” “Huh! Let me see yanzu senayi tunani, zaman da zanyi dan gudanar da tunanin is 2 million sannan inna yanke hukunci sanar dakai zanyi nanma 2 million, kanaji na?” “Inaji Farouq wannan ba matsala bane please karka mata wani abu batada lafiya she is your sister please karka mata wani abu.” “Naji seka fad’a mata karta min misbehaving if not I might lose my patience.” “Okay zan mata ka bata wayar please.” “Kasani each minutes costs N500,000 d’azu kunyi 2 minutes 1 mil kenan.” “Farouq yaushe mukayi 2 minutes ba katse wayar kayi ba?” “Then fine zan kashe wayar-” da wuri Anas ya katse sa, “A’a please kar ka katse I will pay just give her the phone.” “Good” nan ya maido da kallonsa kanta “ke! Gashi sauran kimasa wani munafircin kiga in ban rabaki da shegen dake cikin ki ba.” Hannu d’aya ya since mata tare da bata wayan sannan ya yi gefe guda a d’akin yana me zuba mata ido. “Flower kinaji na?” cewar Anas. Cikin sautin kuka ta amsa “eh Habeebi.” “Good kibar kuka kinji? And kiyi duk wani abinda ya buk’ace ki muddin be sab’awa muslinchi ba I promise I will let yo out of there, I love you.” “Habeebi I miss you please karka d’au lokaci kazo ka d’aukeni, I don’t trust Ya Farouq dan Allah Habeebi.” “Flower stop panicking and do as he says I will come in shaa Allah kinji? Kibar kuka zeyi affecting lafiyarki, I love you.” “I love you too Habeebi, I love you so much.” Kafin Anas yasake cewa wani abu Farouq ya fisge wayan “time up!” ya sanar da Anas. “Farouq please ka bata wayan I will pay you.” “Nasani sede kakai limit naka na yau sekuma gobe if you are lucky.” “Please Farouq.” “Why being so insistant? Wallahi ka sake roqana baraka sake magana da ita ba mschw!!” “Okay but please Farouq feed her kabata abinci kasan condition nata zama da yunwa won’t help.” Kallon faracunsa yake sannan yace, “aww! kana nufin wai shegen cikin dake jikinta?” “Eh shi Farouq dan Allah feed her karka barta da yunwa.” “Toh ai banida kud’in bata kalan abincin data saba ci a gidanka ka turo kud’i kamar miliyan d’aya haka se a siya mata abinci me kyau.” “Okay I will do it, zanyi just kar ka barta da yunwa.” “Naji kana cika min kunne zan maka sending acct details d’ina sauran ka b’ata a irgen kud’ina kaga tashin hankali” yana kaiwa nan ya katse wayar nan da nan yatura wa Anas acct details nasa ba tare da b’ata lokaci ba Anas yama PA’nsa magana akayi ma Farouq transfering 7 million yana zaune a gefen Fannah yana gasa mata bak’ak’en kalamu alert yashigo ta wayarsa bayan ya duba ya sakar dawani shu’umin murmushi “wifey mijin nakin nan baya wasa now you can have your lunch tunda ya cika alk’awari” wani number yayi dialing a wayarsa; “Okay angama had’a dining d’in?” “Eh Boss angama komai is ready.” “Good!” nan ya katse. Igiyoyin da yabi ya k’ulle mata jiki dasu yabi ya sissince “tashi muje kichi abinci wifey.” K’in miqewa tayi cike da mugunta ya miqar da ita daga saman hannunta k’ara soai ta sakar haka ba tausayi yajata zuwa wani had’ad’d’en d’akin da aka tsara sa as dining room dogon table ne wanda aka cika sa dam da abinci kala kala wane (feast) kujeru biyu ne kad’ai a both ends na table d’in kujera d’aya yaja mata ya zaunar da ita sannan yakoma nasa shima ya zauna. “Eat my lady duka wannan naki ne kichi babynki yasamu yaci shima kafin in rabaki dashi.” “Ya Farouq mesa kake haka? Me na maka? Yanzu zakaso ache kanada sister sannan wani yana mata haka?” Fork yakai baki “unfortunately banida sister so kichi abinci.” “Kabani dalili d’ayan da zesa inchi wannan abincin, nasani ko kasa abinda ze zubar min da ciki aciki, banaso.” “Wifey kinga karki min rashin kunya anan eat.” “Barin chiba Ya Farouq dan Allah ka fitar dani daga nan ka kaini gida gun mijina please.” Banza da ita yayi ya d’au wayarta ya kira Anas ringing d’aya Anas ya d’ga “hello.” “Mr. Fauzi” “Na’am Farouq baka ga alert d’in bane?” “Nagani kama Fannah magana tadena cika min kunne da surutu I might lose my patience and if that happens zaku iya rasa shegen ku.” “Kabata wayar please I will talk to her.” “Na fad’a maka ka riga kayi exhausting time naku na yau.” “Nasani Farouq ka taimaka please.” Ido yama mutumin dake gefensan tare da miqa masa wayan yakai wa Fannah. “Hello Flower please kichi abincin kinji? Ko kinason abu ya samu babynmu?” Kai ta kad’a wane yana kallonta. “Kinaso?” “A’a banaso Habeebi bansani ba koyayi poisoning abincin.” “Beyi ba Flower in shaa Allah beyi ba kichi kinji? I’m coming for you I love you.” Bata samu tace masa she loves him too ba mutumin ya k’wace wayan. Plate d’in ta jawo tayi bismillah sannan takai kad’an daga cikin pepper soup d’in kifin bakinta a hankali tasamu tad’an cika cikinta fargaba ya hanata k’oshiwa. Bayan sun gama ya buk’ace ta data bi bayansa. “Ya Farouq kai baka Sallah ne? Dukda bansan k’arfe nawa bane amman nasan Azahar da La’asar sun wuceni.” “Ohh wifey ni ai banayi had’asu nake duka se isha zan yi amman tunda kince haka taho in rakaki” bejira tace komai ba yaja hannunta zuwa d’akinsu daya tanar masu har cikin bayin ya rakata “ko kinason kiyi wanka?” “I wouldn’t mind tunda ba a cikin k’azanta ka d’aukoni ba” tabasa amsa tana me k’arewa bayin kallo mamaki ne yacika ta shin ina Farouq yasamu kud’i haka? Daya karanchi hakan seya murmusa “mamaki kike? Karki damu ba sata nayi ba bashi na karb’a kuma har na miyar musu da kud’in da Anas yaturon” sede har a yanzu bata bar kallonsa ba nufin bata da yarda ba. “Wallahi kuwa wifey ko mamakin ya akayi nasan gidanku kike? LOL long story;” _“Da barina prison yanzu sati biyu kenan bashin danaci na yi mana wannan siyayyan shine wanda Baba yayi amfani dashi yayi bailing d’ina kuma drugs ne source na kud’in. Inada wani abokin dake siyar da coccaine shine yabani bashin miliyan 5 dashi na aiwatar da komai. Bayan fitowana da kwana biyu na shirya tsaf naje Enterprise na Habeebinki namusu k’arya cewa business man ne ni ina kuma neman appointment dashi sam receptionist d’in ta hanani ganinsa saboda nak’i bata personal information akaina, me gadin wajen nasamu na tsara sa har seda ya fad’amin k’arfe nawa Anas yake tashi daga office anan ne nasamu nayi timing nasa bayan da aka tashi na biyosa anan ne na ga gidanku. Dalilin dayasa nasan rana kinfita kuma bada Anas ba kuwa itace yawan zama dana keyi a unguwanku ganin driver yazo ya d’aukanku naje na shirya nima, dawowa na yayi daidai da shigowarku achan na tsare driver bayan ya ajiyeki namasa tsinannen duka dan k’in bani had’in kai dayayi, seda nayi pulling masa bindiga ya yarda yakaini ciki. Dana jima da kashesa sede kuma naji anacewa security doors ne a gidan naku inba wanda yasani ba baya bud’uwa._ Any question wifey?” Kai kawai take kad’awa tana tausayawa d’an uwan nata kalan rayuwar daya d’au ma kansa. “Allah shiryeka Ya Farouq inhar kaid’in me shiryuwa ne shikuma Moosa daka rufesa a d’aki so kake ya mutu ne? Ka tuna d’an Adam ne shima mejin yunwa.” “Karki damu wifey your wish is my command yanzu yi wanka abinki cikin wardrobe akwai kaya seki zab’a d’aya ciki kisa, I love you.” Tsuka taja “wifey I said I love you.” “I hate you Ya Farouq na tsaneka.” Bakinta ya maquro “what did you say?” “I said I hate you, ka sakemin fuska mugu kawai” tahau kai masa bugi. “Quit it!” Ya daka mata tsawa. “Kin d’au wasa nake ko?” Hannu yasa ya yage mata hijabi tun daga sama har k’asa kafin ta hankara ya had’a ta da bango tare da kai hancinsa wuyanta yana wani shunshuna mata jiki. Hannayenta daya matse jikin bangon take ta k’ok’arin k’watansu amman takasa. “Ya Farouq dan Allah kabari” ganin yasoma wuce gona da iri ta qurma wani irin ihu dukda haka be dena gudanar da abinda yayi niyyah ba dabara ce ta fad’o mata k’afanta ta d’aga ta saita daidai abinsa takai masa bugi da k’arfi wani erin k’ara ya saki cike da azaba take a wajen ya durk’ushe anan ne tasamu ta k’wata kanta tare da d’ago hijabinta tana kare k’irjinta dashi. *© MIEMIBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:58, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 8⃣2⃣ Anas besan lokacinda ya fasa glass cup dake hannun saba daga riqo tsantsan wani irin baqin kishin daya tokaresa jin abinda Farouq yama Flowersa, kasancewar fatar jikinsa bame k’arfi bane take glass d’in yamasa kaca-kaca da hannu. K’ara Ummie da Amal suka sakar ayayinda Abuu da Shettima sukayi kansa suna tattara broken glasses d’in. Idanunsa take sukayi wani irin wawan jaaa a yayinda zuciyarsa ke wani erin tafasa. Amsar wayan Farouq yayi daga kunnen crying Fannah “Mr. Fauzi kaji ka gaskata zance na?” Cikin wani erin muryar da ban tab’a sanin Anas dashi ba yayi maganar “Farouq kaji na rantse I WILL KILL YOU WITH MY OWN BARE HANDS kawai kajira had’uwa na dakai.” “Hohoho!!! Kafin ka kasheni nikuma zana kashe maka Flower I have to go kasan akwai aikin abortion gabana” yana kaiwa nan ya katse wayar koda Anas ya gwada kiransa back cemasa ake the number does not exist kasancewar Farouq ya karya sim d’in yakuma kashe wayar gabad’aya ya cire battery bare sake amfani dashi ba gudun kar ayi tracking nasa down. Haka yayi da wayar Fannah ma ya cire sim nata ya karya yakuma kashe wayan. Wasu erin zafaffun hawaye ne suka soma sauk’o ma Anas akan kumatu. Waje Ummie tayi da Amal ganin Anas na kuka again. Daidai Abuu ya bud’e baki zeyi magana kenan wayar Anas ya soma ruri Abuu nakai dubansa yaga Mami. Kafin ya d’aga ya kalli Anas ganin ko kad’an hankalinsa bai jikinsa ya d’aga wayar kawai. “Hello Maman Fannah.” “Assalamu Alaikum” tace. “Wa’alaikis salam Abban Anas ne.” “Ayyah ina wuni?” Ta gaishesa. “Lafiya alhamdulillah” ya amsa. “Ya kowa da kowa?” “Duk k’alau.” “Masha Allah nace ko Anas na kusa inason muyi magana ne da Fannah nayita kirar wayarta bata d’agawa.” Zuciyarsa yaji yayi dum! Ya buga yama kasa magana. “Hello...?” “Maman Fannah inason ki saurareni dakyau dan Allah kuma kisani muna kan bakanmu na neman Fannah baramu tsaya ba semun sameta.” Gaban ta taji yayi mumunar fad’i. Bayan salatin data sakar cike da tashin hankali tayi k’arfin hali tace, “Abban Anas meya samu ‘yata dan Allah?” “Ki kwantar da hankalinki please, ‘yar ki Fannah ta na wajen Farouq yanzu haka as we speak...” Nan ya kwashe labarin komai yabata. Salati take alokaci guda idanunta suka ciko da hawaye. “Yaushe Farouq da mahaifinsa zasu fita harkar Fannah subarta taji dad’in rayuwa? Me tayi musu?” Hak’uri Abuu ya riga bata sannan daga bisani ya katse wayar. “Anas ka kwantar da hankalinka kaji?” “No Abuu I can’t.” Ya fad’a rai a b’ace. Hannunsa daya yayyanke Shettima yayi yunk’urin tab’awa “don’t touch me Shettima just leave please both of you dan Allah kufita min a d’aki am sorry please.” Kai kawai Abuu ya girgiza he understands exactly what his son is going through. “We will Babana zamu bar maka d’akin just behave yourelf, Shettima mu fita.” Nan suka fice, hankalain Shettima ya matuqar tashi kasancewar yasan halin wan nasa sam be iya rungumar k’addara ba tsoronsa kar Anas yakoma shaye shaye irin na da. Bayan ficewansu Shettima Anas ya miyar da kallonsa kan hannunsa me zuban jini alokaci d’aya ya miqe yashiga bathroom sabon spirit ya bud’e ya bulbula kan hannun nasa k’ara ya saki sosai dan sharp pain dayaji,gritting teeth nasa yake dan azaba idanunsa matse gagam. “Atleast I can feel kad’an daga cikin pain da kike feeling Flower, atleast you are not alone in this, atleast zan iya feeling koda half of your pain.” Fuskarsa ya d’ago yana kallon mirror instead yaga fuskarsa se fuskar Fannah kad’ai yake gani ciki, tunaninta duk yabi ya mamaye masa k’wak’walwa. Da tunanin abinda Farouq ya sake hitting masa k’wak’walwa kuwa besan a lokacin da ya shure kwalabai da robobin mayukan shafe-shafe da suke kan counter d’inba. “Fannah *_TANA TARE DA SHI_* No! he can’t take away Fannah from me, Fannah is mine, Farouq I will hunt you down like an animal.” A fusace yabaro bayin besan a lokacin daya ciro wani dogon kara daga k’ark’ashin gadon sa ba yasoma fashe fashe daga kan TV, dressing mirror, hanged mirror ba abinda be fasa ba. Abuu dake parlour ne jikinsa yabasa ba lafiya ba agurguje ya bud’e k’ofar d’akin ya tarar da Anas d’auke da wuk’a yana kan tsaga tafin hannunsa se cize bottom lips nasa yake cike da azaba amman hakan be hanasa cigaba da gudanar da abinda yakeyin ba. “ANASSSS!!!!” ya kira sunansa diabelievingly a yayinda su Ummie ke bayansa suna sakar da salati kansa Abuu ya nufa ya tsinka masa mari tas kukeju take Amal ta b’uya bayan Ummie. “Bakada hankali ne iyyeh? Whats all this?” Yayi maganar yana k’are kallo wa mess da Anas yayi wa d’akin. “Ina ka kai hankalinka?” Hannu yasa ya k’wace wuk’an. Se anan Anas yayi magana; “Abuu give me back kabani please, be kamata inbar Fannah kad’ai tana shan wahala ba kabani wuk’an kaga se muna feeling pain d’in tare.” “Anas get your senses together kanajina koh?! What nonsense. Nasan wannan abu ne meh wuya amman hak’uri zakayi kamar yadda nayi nima da Ummiminku ta tafi ta barni, balle ma kai ba tafiya Fannah tayi ba kidnapping nata akayi kuma in shaa Allah zamu sameta meye amfanin wannan abubuwan da kakeyi iyyeh? It has to stop!” Ummie ce tasa baki; “A’a Ya Ibrahim kamishi uzuri, wannan tsaka che me wuya shi kad’ai yasan yadda yakeji kaima kasan how it feels like. In zaku bani dama kufita ku barni dashi” nan ta k’ariso cikin d’akin da Amal biye da ita batare da Abuu yace komai ba yafice haka Shettima ma. “Amal kema bisu.” “No Ummie please kibarni in zauna da Ya Anas” dagudu taje ta rungomoshi tana hawaye. “Ya Anas in shaa Allah zamu samu Fannah wannan mugun Farouq d’in bare mata komai ba, bare mana harming baby ba because we love our baby ba?” Sam be amsata ba kai kawai ya gyad’a mata daga baya a hankali nan da nan Ummie ta gyara masa kan gado suka hauro dashi ita da Amal. D’akin tashiga tattarawa ayayinda Amal ta aza kan Anas a cinyointa tana shafa gashin kansa a hankali bayan ta tare jinin dake d’iga daga hannunsa da tissue. Bayan Ummie tagama kimtsa d’akin ta taho da bowl d’auke da towel ciki d’an k’ananun yankan da Anas yajijji a jikinsa agarin fashe fahsen dayayi dakuma yankan dayaji wa kansa ta goggoge tayi treating masa cikin k’ank’anin lokaci ta kimtsa sa. “Zakaci abinci Babana?” Ta tambayesa shiru yayi be amsata ba hakan ya tabbatar mata baya jin yunwa. “Amal taso mu basa waje kinji?” Seda ya bari Amal ta mik’e sannan ya rik’e hannunta “ki zauna kinji Angel, don’t leave me too.” “Ya Anas I will never leave you *_INA TARE DA KAI_* kamar yadda Ya Fannah ma take *_TARE DA KAI”_* calming and soothing wors masu kwantar da hankalin d’an Adam Amal ta riga furtawa yayanta tana sake tabbatar masa dacewa Fannah tasa ce kuma zasu same ta, shi ya jasu sallan isha sam yak’i barinta ta fita daga d’akin cemata yayi a d’akin yakeson ta kwana ita akan gado shi kan couch*** Baa tare da b’ata lokaci ba Mami tasamu Baba ta gaya masa halin da ake ciki hankalinsa yayi matuk’ar tashi tuni Afrah da Aiman suka soma kuka Mami na mara masu baya. Ya Khaleel Baba ya kira sam munafikin Allah ya nuna masa besan halin da ake ciki ba ce musu ma yayi rabonsa da Farouq sati d’aya kenan yanzu. Suna gama wayar ya kira Farouq ya sanar dashi. Dariyan bosawa Farouq ya sakar “barsu Baba basuda hankali ne karka damu inada miliyan 2 yanzu sauran miliyan uku daga nan se muyi proceeding plans namu” “Kayi daidai Farouq danko Fannah taka ce tun kana d’an yaro kake santa.” “Maganar ka dutse Baba will get back to you later” nan ya katse. Maido da kallonsa yayi kan crying Fannah cike da azaba ya d’agota daga saman hannunta, mijinki is trying my patience you will have to bear the burden janta yayi zuwa d’akin d’azu tana had’asa da Allah amman ko sauraronta beyi ba d’aureta ya kuma yi sede wannan karan be toshe mata baki ba. Wani samsung S5 yaciro ya d’auketa hoto sannan yabi ta whatsapp yayi sending takan Anas yasan sarai Anas ba shiga whatsapp zeyi ba dan haka yamasa sending SMS _Hurry! Smart guy and check in your whatsapp_ Amal ce ke kusa da wayar alokacin da saqon ya shigo. “Ya Anas you have a new message.” “Barshi Angel am not in the mood.” “Ya Anas inkuma ya shafi Ya Fannah fah?” jin ba k’arya a magananta ya miqe tare da amsar wayar bayan ya karanta hankalinsa ya sake tashi fiye dana da ba tare da b’ata lokaci ba yayi enabling cellular connection first message da yayi popping up ya bud’e ganin pictures na Flowersa hannaye da k’afafunta a d’aure kansa yayi wani erin mumunar bugawa, hannu yasa ya dafe kan nasa ta gefen migraine d’in. Cike da tashin hankali Amal ta matso kusa da shi tana dafe sa, “Ya Anas mene ne? Meya faru?” Kasa koda furta mata ‘A ’ yayi. Ba tare da b’ata lokaci ba yakira layin karap Farouq ya d’aga. “Hello smart guy now what? Zakayi as I say kokuwa I need to let her suffer some more?” “Farouq please let her go ka saketa dan Allah kai bakasan darajan ‘ya mace bane? Musamman ma me d’auke da juna biyu?” “Bansani ba kuma banason sani do as I say and I will let her go.” “You filthy son of a b*tch what the f*ck do you want? Meh kakeso?! ” Amal dake a gefensa seda taja da baya tsabagen firgita datayi dan kalan tsawan da Anas ya daka. “Zamuyi magana if you are ready, I’m hanging up.” “Kafad’a min meh kakeso and let her go.” “Miliyan uku nakeso... For now.” “Are you crazy Farouq?” “Yes I am, zakayi transferring kud’in kokuwa haka kakeson Fannah ta kwana?” “I will zanyi please ka saketa please.” “Ka turon kud’in first.” “Nace zan maka sending ka sake ta please.” “Senaga alert” nan ya juyo yana kallon Fannah dake ta kuka ba sauti. Fuskarta ya shafa “Farouq please kadena tab’ani banaso.” Maganarta har kunnen Anas. “Farouq me kake mata? Kadena tab’a ta please.” “Meh aciki dan na tab’a wifey na?” “Kai wai bakasan tab’a macen da muharramarka haramun bane?” “Bansani ba kuma banason sani send me my 3 mil and I will let go your wife.” “Son of a b*tch” cewar Anas sannan ya katse wayar nan da nan yama Kacallah magana aka mai transferring kud’in. Kacallah na sanar da Anas yayi transfer d’in yakira Farouq back sede sam layin yak’i shiga kodaya gwada trying na Fannah ma haka, hankalin Anas in yayi dubu be tashi ba he can’t wait gobe a fara investigating, fatan ranan had’uwansa da Farouq kawai yake. **** “Mijinki d’an Amanah Fannah har ya turo kud’in” cewar Farouq alokacinda yake since mata hannu. “Muje muci dinner.” “No way! Ya Farouq I have to pray first.” “Ba matsala zaki iya yin duk wani abinda kikeso tunda mijinki ya cika min buri.” “Burin meh?” Ta tambayesa tana shafa hannunta daidai wajen daya d’aure har seda yayi pink.” “Karki damu sooner zan sanar dake shiga kiyi alwalan ina jiranki.” Tsuka taja sannan ta shige bayan tafito ta had’a Maghrib da Isha yana zaune yana jirarta ko ajikinsa ma beyi Sallah ba, bayan ta idar yajata da hannu zuwa dining room nasu achan sukayi having dinner. “So wifey time to sleep koh?” “Kamar ya time to sleep?” “Ya kike kwana da Anas?” “Ya Farouq shin wai bakasan Anas miji na bane? Kaikuma ba muharrami na bane saboda haka barin had’a kwanciya dakai ba.” “Kinsan me nafiso? Nafison kina fighting d’ina haka ‘cause it gives me more and more reasons to fight you down, dani zaki kwana ko kinaso ko bakiso.” A fusace ya miqe ya doso gabanta tare da miqar da ita da hannunta. Hannun nasa ta hau bigewa “ka sakeni Ya Farouq let me go.” Ko saurarenta beyi ba haka yajata sama zuwa d’akin daya tanadar masu akan gado yayi wurgi da ita. Kuka take sosai. Kayan jikinsa ya hau cirewa boxers zallah yabari. “Ya Farouq dan Allah na had’aka da Allah kayi hak’uri ka kaini wani d’akin in kwana dan darajan manzon Allah.” “Zaki ajiye wannan mayafin agefe ne kokuwa?” Sake matse gyalen tayi ajikinta ganin batada niyyan cirewa ya nufeta tare da jan gyalen seda ya rabata dashi ihu tahau yi tana kiran sunan Anas. Dukiyar fulaninta ya cafko wani irin k’ara ta saki sannan daga bisani ta tsinke sa da marin da bai expecting ba. Cikin kuka take maganar “bakada hankali ne Farouq?” Yau ko yayan ma babu. “Wallahi the next time ka gwada yunk’urin tab’ani I wont hesitate to kill you mugu, azzalimi maras imani kawai wanda besan darajar mace ba Alla-” bata k’are maganar ba ya kawar da ita da mari. “Ni kika d’aga hannu kika mara dan fitsara? Sa’arki ne ni? You are asking for it.” Hannunta ya ja be tsaya ako ina ba se wani d’akin da ba komaj ciki banda uban duhu da poles guda uku ciki. “Ya Farouq ka sakeni mugu, azzalimi kawai ka sake min hannu” wani marin ya sake kai mata anan seda gefen bakinta ya fashe. A k’asa kusa da d’ayan pole d’in ya yasar da ita sannan ya d’ago wani thick igiya ya d’aure mata hannayenta duka biyu daga baya ihu sosai ta rigayi dan yadda ya matse mata hannayenta bibbiyu a bayan pole d’in sannan ya k’ulle da k’arfi gabanta ya sha ya k’ulle k’afafun ma sannan ya matso da fuskarsa gab da nata bata bar kukan ba har yanzu “Ya Farouq dan Allah kayi hak’uri ka sakeni please.” “Mu kwana lafiya kikace min a’a ba? Haka anan zakiyi spending night naki alone in this room.” Nan zuciyarta yawani buga tunda take bata tab’a kwana ita kad’ai ba se yau ita ina ma d’aki ne me fasali da dasauki. “Ya Farouq dan Allah kayi hak’uri.” Fuskarta ya riqo sannan yasoma laluban lips nata dawuri ta maqesu chiki haka yatayi amman tak’i barinsa yayi kissing nata, daya gaji ya d’auko cellotape ya manna mata a bakin “sleep tight wifey” yace mata tare da kashe wutan d’akin wani erin baqin duhu ne ya ratsa cikin d’akin alokacinda ya bankad’e k’ofar. Kuka take sosai tana ta murza hannayenta ko zata iya sinche igiyiyin amman takasa haka yadda taga rana taga dare seda gari ya soma wayewa ne tasamu wani wahalallen baci yayi awon gaba da ita. Shegen se 9:30AM ya tashi ko Sallah baiyi ba, bashin da ake binsa jiya ya sauk’e Asuba da Azahar kad’ai sauran se anjima in ya samu time. Bayan yayi wanka ya shirya cikin black top da jean trousers sannan ya nufa d’akin Fannah har a lokacin bacci take, tsugunawa yayi a gabanta fuskarsa d’auke dawani murmushin tsiya. Ba abinda yake kalla a fuskarta banda lips nata tsabagen k’azanta ko brushing Fannah batayi ba amman ahakan yakeson yayi kissing nata. Fuskarta ya shafo a hankali ganin batako motsa ba ya sake matsoda fuskarsa gab da nata ta yadda nishinsu ki tinkling. Abu k’iris ya rage yayi owning lips nata ta bud’e idanunta lokaci guda. Wani irin nishi taja tare da warwaro idanunta, baya yayi kad’an alokacin dayaga ta maqe lips nata. “Good morning wifey da alama you had a wonerful night” ya k’are maganar yana since mata igiyoyin. Ganin batada niyyan masa managa ya cigaba “muje kiyi wanka ina neman shawararki.” “Kayi duk abinda kakeso daman ka tab’a neman shawara na game da abu?” “Wifey mesa kike min haka ne? Kullum bakida abinyi banda fad’a dani mijinki?!” “Niba matarka bace kamar yadda kaima kake ba mijina ba.” “Nasani ai shiyasa nakeson muyi aure, auren sunnah.” K’irji ta dafe “aure? Ya Farouq dan Allah ka rufa min asiri taya zaka aureni bayan inada igiyan aure akaina??” “Wannan duk ba komai bane, zamu bar Nigeria zamu koma ko Ukraine ko Ghana seki zab’i k’asan da kika fiso.” Hawaye ne suka soma ambaliya kan fuskarta... durk’ushewa tayi har k’asa a gabansa jin ya ambaci barin k’asa gabad’aya. Rok’ansa ta soma “Ya Farouq dan girman Allah kayi hak’uri dan soyayyar da kake ma manzon Allah kayi hak’uri kaji k’aina karka kaini wani k’asa daban karka rabani da iyayena dan Allah Ya Farouq...” Ta k’are maganar cikin sautin kuka. *Ina me baku hak’uri da posting da bana samunyi kwana biyu my phone is having a problem, ku k’ara hak’uri I love you guys so much* *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:58, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 8⃣3⃣ “Haba! wifey me yayi zafi haka? Tashi please I’m trying to change your future.” “Ya Farouq dan Allah karka gudu dani zuwa wani k’asa daban please.” “Kinsan me wifey? Wannan had’ani da Allahn da kike ba tasiri zeyi akaina ba ki tashi kiyi Sallah muyi breakfast inkuma se anjima zakiyi sallahn then muje mu karya.” “No Ya Farouq! Allah yafika mugu, azzalimi maras imani kawai wallahi baraka gama da duniya lafiya ba, you are going straight to hell such a demon.” “Ki kirani da duk wani sunan daya miki abu d’ayan da nakeson kisani shine ke TAWA CE! YOU ARE MINE!” bejira ta sake magana ba ya finciko ta da hannunta ta sama be direta a ko ina ba se abayin d’akinsu “na baki minti goma kuma” yana kaiwa nan ya ja k’ofar ya rufe. Kuka me tsuma rai takeyi tafi minti biyar tsugune a bayin sannan daga bisani ta miqe tayi brushing sannan tayi wanka da alwala, kayan jikin nata ta miyar sannan cike da tsoro ta fito mayafinta na jiya ta gani a k’asa dashi tayi Sallah tariga roqan Allah daya kareta daga sharrin Farouq. Bada jimawa ba Farouq ya dawo d’akin zaune yasameta ta d’aga hannu sama tana addu’a, waje yanema ya zauna tare da zura mata ido har seda ta tofe. “Excellent ina fatan kinyi addu’an Allah sa d’an cikin kin me cetoh ne.” Cikin dashasshiyar muryar tace, “me kake nufi Ya Farouq?” “Zubar da cikin zanyi bazeyi mu tafi dashi Ukraine ba chan inda na yanke hukuncin zamu, I want us to start a new life.” “Nasan ba point rok’anka amman dan Allah ka rufa min asiri karka min haka Ya Farouq na rok’eka please kamin rai.” “Wifey fa ba ke nace zan kashe ba shegen abinda ke cikin ki nace zan kashe” ya nuna cikin nata da yatsa. “Before then muje mu karya inajin yunwa.” “Banaji kaje ka karya kai kad’anka” ta k’are maganar hawaye na ciko mata a ido. “Wifey kinga banason taurin kai nace muje mu karya” bejira ta amsa shiba ya fisga hannunta be direta a ko ina ba se akan dining chair nata “eat wallahi ko kici ko in zubar da cikin nan at this instant.” Shiru tayi bata amsashi ba, bara kichi bane sena zubar da cikin komeh??” “Meh amfanin chin abincin? Ko nachi ko banchi ba bashi ze hanaka aiwatar da abinda kayi niyyah ba.” “No wifey” ya shafo fuskarta wanda tuni ta bige hannun nasa. “Kichi barin zubar ba.” Idanunta ta d’ago tana kallonsa da nufin bata yarda ba. “I swear wifey, kichi barin zubar ba, ki k’i chi in zubar.” “Kabani reason d’aya da zaisa in yarda dakai.” “Because I’m Farouq, now eat.” Fork d’in ta d’aga tasoma ci bayan tayo bismillah se anan ya koma nasa b’angaren dining table d’in shima yasoma chin nasa kamar jiya yau ma fargaba ya hanata chin abincin sosai kad’an tachi taji ta k’oshi. Bayan da yagama chi ya sake janta zuwa d’akin nasu tare dayin wurgi da ita a k’asa, wardrobe ya bud’e tare da ciro wani powdered substance fari k’ulle cikin leather. Tana gani jikinta yabata abin zubda cikin ne kuka ta soma papawa. “Ya haka sekace kinga mala’ikan mutuwa?” Kai kawai take kad’awa tana baya-baya. “Ya Farouq dan Allah kayi hak’uri.” Hannunta ya cafko “kinga karma kibani wahala ki bud’e bakinki kisha wannan dakanki if not zan d’ura miki na k’arfi da yaji.” “Ya Farouq I beg you dan girman Allah.” Ledar ya bud’e “ungo gashi” sam tak’i karba. Kad’an daga cikin maganin yasa a hannunsa tare da maquro fuskarta “bud’e bakin bud’e nace!” gamme bakin nata tayi se buginsa take a k’irji haka seda ta zubar da maganin hannunsa dana ledar duka a k’asa dan shuresan data tayi. “Ke?! Bakida hankali ne? Maganin kika zubar?” Wani wawan mari ya kai mata “tunda kince bara abi hanya me sauk’i ba by the time na miki fyad’e anan shegen cikin naki ze zube.” Bugata yayi da jikin bango yasoma sunsunar wuyanta yana bin jikinta da filthy harshensa k’afanta ta saita takai masa bugi a daidai manly place nasa fiye da na jiya. “Arrgghhh!!” Ya sakar da wani irin wahalallen k’ara tare da durk’ushewa da gudu ta bi ta gefensa mayafinta daya riqo tasa hanu ta fisge da sauri tasa gudu se k’olla mata kira yake amman sam tak’i juyawa a gurguje tafito daga d’akin ta inda taga staircase tabi wajen. Har a yanzu hannunsa na a rik’e a wajen nasa jikin bango yake dafawa har yafito daga d’akin. “Guards! Securities! restrain her!!” yayi maganar da ihu, k’ara gudun ta tayi bayan ta sauk’o last floor d’in ta dosa babban k’ofan data gani, chan tayi kicib’is dawani giant mutumi bak’i k’irin wane an pentasa, baya tayi da wuri ayayinda yake takowa gabanta. “Bawan Allah dan Alkah kayi hak’uri ka rufa min asiri kabarni in gudu dan Allah...” tana maganan tana ja da baya gum! Taji jikinta ya had’e dana mutum a hankali cike da tsoro ta juya fuskar Farouq tagani nan tashiga wani sabon b’arin. “You can never escape from me you stupid” yakaura mata mari. “Take her Joseph kaje ka k’ulla min ita da chains ka kuma rufe min bakinta.” “Ya Farouq dan Allah kay-” bata k’are maganar ba Joseph ya sab’ata a kafad’arsa achan yaje ya k’uk’k’ulleta**** *ANAS* 10:45AM Amal ce tsaye akansa yana zaune bisa Sallaya se kuka yake ba makawa, “Ya Anas dan Allah kukan nan ya isa bayida amfani ko bacci fa bakayi ba through out jiya da daddare nafilfili ka rigayi da garin Alkah ya waye yanzu kuma barakayi bacci ba? Please is okay in shaa Allah zamu sami Fannah kabar kukan please.” “Angel how?” Abinda bakinsa ya iya furtawa kenan, “taya zamu sameta bayan bamu ma iya reaching nata duk layin da nasan zan iya samun Farouq na kira basu shiga and I have no idea ina zan sameta bansan wani hali take ciki ba Amal.” Bayansa tahau bubbugawa “is okay Ya Anas zamu sameta in shaa Allah.” Daidai nan Ummie tashigo ma Anas da breakfast haka sam yak’i chi danko bayida appetite ko kad’an, inbega Fannah ba bai tunanin ze iya sake chin abinchi da k’ak’ani k’ak’a Ummmie tasamu yaci kad’an bayan yayi wanka suka fita police station dan fara investigating al’amarin. Daga gidansu Fannah suka fara inda akyi ma su Mami da Baba tambayoyi da dama cikin wuni d’aya Mami ta fita hayyacinta ta canza kamanni gabad’aya. Waya akasa Baba yayi wa Ya Khaleel bayan ya d’aga aka had’asa da police fitsari ne kawai beyi ba daga jin muryan police. Minti goma kacal aka basa da yazo sa gidansu Fannah if not za’a iya using rashin zuwansa against him ayi arresting nasa. _8 minutes later..._ Daidai nan shigowar Ya Khaleel sekace salihin asali sewani behaving innocent yakeyi tambayoyi da dama aka masa wanda duk ciki be bada amsa d’ayan daya kasance gaskia ciki ba, “ya akayi Farouq yafito daga gidan yari?” “Bansani ba wallahi ranka shi dad’e.” “When last rabuwanka dashi?” “Sati uku da suka shud’e kenan yanzu, tun daga ranan dana kai masa visit dana sake komawa washegari akace min anyi bailing nasa nata gwada layinsa bana iya samunsa, ku tayani nemo d’a na please.” “Are you sure Mr. Khaleel danko kamana k’arya zamuje mu duba record.” “Www... Wallahi Ba k’arya nake ba” ya k’are maganar yana had’a gumi. Ko da aka buk’acesa da ya kawo wayarsa aduba aga, ba fargaba ya bada saboda Farouq ya fad’a mai aduk lokacinda sukayi waya yana deleting logs nasa dan haka ba’a samu aka gano wani abu ba. “Abuu wallahi he is lying he is definately lying yasan duk wani whereabouts na Farouq b’oyewa yake munafikin Allah kawai.” “Haba Anas d’ana-” katsesa Anas yayi “shut the f*ck karka sake misantani da d’anka criminal ass kaji na rantse Ya Khaleel kome kake wallahi in na gano you also have something to do with the disappearance of my wife I won’t hesitate to kill you da hannu na zan kashe ka irresponsible father kawai.” “Nasan da ky-” be k’are maganar ba Anas ya mik’e a fusace tare da shak’uresa jikin bango “ina Farouq yakaimin Fannah?! Tell me! Ina yakaita?!” Abuu ne dasauran police d’in suka yi sauri suka k’wato Ya Khaleel kafin Anas yayi masa illa, d’an banza tuni nishinsa ya canza idanunsa suka wani fito waje dan azaba. *FANNAH* 1:50PM A hankali aka bud’e d’akin da aka rufeta ciki, a firgice ta maida kallonta wajen idanunta suna tsiyayar hawaye. Bak’in fuska taga d’auke da abinci da ruwa a hannayensa nan tashiga rawa daidai gabanta mutumin ya ajiye abincin tare da since mata bakinta da hannu d’aya yace “ga abincinki inji Boss kichi.” Seda ta bari yakai bakin k’ofa sannan takirasa da “bawan Allah” chak ya tsaya. “Wani abu ne?” Ya tambayeta tare da kewayo wa. “Bawan Allah muslimi ne kai?” “Eh me kika ga?” ya bata takiacaccen amsa. “Masha Allah k’arfe nawa ne dan Allah?” Bayan ya duba agogon hannunsa yace, “1:52PM” numfashi ta saki “dan Allah ka sinceni inyi Sallah banyi Sallan Azahar ba.” “Boss bece in sinche ki kiyi Sallah ba so eat insamu inbar nan.” “Be fad’a ba amman ai kai kasan haqqin Sallah dan Allah ka sincheni.” Wayarsa yaciro ya kira Ya Farouq alokacin yana a airport yana proceeding abubuwan tafiyansa Ukraine da Fannah dakuma Ya Khaleel kasancewar yasamu passport nata acikin jakarta. “Hello Boss gata nan na kawo mata abincin amman tace setayi Sallah.” “Karka damu kabarta tayi amman ka tabbata kana tsaye a kanta har tagama okay?” “Okay Boss” “Good bayan ta gama kuma ka kuma d’aureta karku bari tayi escaping.” “Angama Boss” yana gama wayar ya maidashi cikin aljuhunsa sannan ya nufo gabanta ya sinche mata chain d’in da kwad’on da aka datse. Kamar wanda k’wai ya fashe ma aciki ta shiga bayi tayi alwala sannan tayi Sallah duk mutumin na kallonta, jira yake taci abincin yayi tafiyarsa amman tak’i koda bud’ewa. “Hey Miss kiyi ki ci abincin mana banason wasan cha-chan nan ya wuceni fah.” “Kayi tafiyar ni barin chi ba.” “Suits you right” nan ya mik’e ya kamata ya k’uk’k’uleta again hawaye take sosai “bawan Allah nasan da akoi ragowar imani a tattare dakai dan Allah ka taimaka min nakoma gun mijina dan Allah nace.” “Allah sarki kyakkyawar hallita sede yadda kika gannin nan barin iya cin amanan Boss d’ina ba” yana kaiwa nan ya fice haka tata kuka gawani erin bak’in yunwan da takeji. Har Sallan Maghrib Farouq be dawo ba kamar d’azu ya tura MB daya kawo wa Fannah dinner anan ne daya sinche ta tayi alwala ta had’a La’asar da Maghrib sede yunwa takeji sosai yanzu dan dole tad’an tab’a abincin. Tana cikin chi wayar MB yasoma ruri a hanzarce ya d’aga “hello Mazzaaa yaneh?” On the otherisde aka amsa “gani nan fah ina cikin gari wallahi harka ya taso kana ina?” “Ohh boi! Ina nan bayan gari ta wajen gidan man Mobil.” Gidan man Mobil? Fannah ta nanata a ranta dad’a kasa kunnenta tayi tana sauraronsa. “Mobil wanne d’aya kenan Mazzaa?” cewar abokin nasa. “Mobil daya d’auki hanyar barin Maiduguri mana ta Yobe.” “Oh okay toh zan iso semu had’u.” “Okay toh ina jiranka” nan ya katse wayar tare da kewayo da kallonsa kan Fannah, yi tayi kamar bata masan yana kallontaba se chin abincinta take a hankali. “Hey Miss ko Mrs kike kiyi sauri kina b’ata min lokaci.” “Nagama tace dashi ba imani kaman d’azu ya sake k’uk’k’ulleta sannan yayi tafiyarsa. Tunanin ya zatayi tasamu waya tayi texting wa Anas location da take yanzu take tunda tagano location d’in, sede sam takasa batasan ina zata samu waya ba duk masu ma Farouq aiki zuciyarsu a karye suke kamar nasa. *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:59, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 8⃣4⃣ 9:30PM Farouq ya dawo gida all tired and exhausted kayan jikinsa ya rage, ya ragar da singlet da shorts zalla sannan yachi abinci. “Ya MB Fannah tachi abincin kuwa?” “Eh Boss tachi dinner amman tak’i chin lunch.” “Good ashe dama nasa mata maganin zubda cikin aciki koda shike nasan yadda zanyi na zubar da cikin.” ya sakar dawata muguwar murmushi. Bayan ya gama chin abincin ya nufa d’akin dayasa aka d’auretan, zaune ya sameta tayi shiru abin tausayi. Tana ganinsa tahau b’ari k’ok’arin magana take amman kasancewar bakinta arufe ta kasa, hannu yasa ya b’antare cellotape d’in yana wani shafa kan lips nata ganin bata maqe lips natan chiki ba bata kuma hanasa yi ba yasa sa shiga duhu. Meke faruwa? “Ya Farouq please ka kunche min hannu nagaji dan Allah” tayi maganan cikin wani erin salo da siririyar muryarta me dad’in gaske. Ba musu bale gardama ya bud’e padlock d’in ya since ta. “Ina kashiga yau Ya Farouq?” tayi maganar ba yabo ba fallasa. “Naje processing mana abin international passport d’innan ne did you missed me?” Kai ta gyad’a, dad’i sosai sokon ya jiyo. “Well am here.” “Ya Farouq akwai wata maganar da nakeson muyi dakai dama.” Ta k’are maganar da ‘yar murmushi kwance kan fuskarta. “Mene ne wifey tell me.” “A farko inason baka hak’ui game da abinda na maka d’azu kayi hak’uri bayan nan sekuma batun barin Nigeria dakace zamuyi na zauna nayi tunani tun ba yau ba nakeson zuwa k’asar nan Ukraine nayi nayi da Anas yakaini amman yak’i bature yace oppurtunity comes to life at once so banason missing wannan oppurtunity na yarda zan bika.” Kamar amafarki yake jin zancen. Idanunsa a waje yayi maganar “Fannah? Anya kece kuwa?” “Sosai nice Ya Farouq zan bika Ukraine.” “Why the sudden change?” “Kamar yadda na fad’a maka na zauna ne nayi tunani.” “Oh sweet wifey” ya shafa fuskarta na d’an lokaci ganin bata hanasa ba yasake jin dad’i shi da kansa ya zaro hannun nasa daga baya. “Wifey ina ba wasa kikeson min da hankali ba koh? Dan wallahi nagano tricking d’ina kike me hanani illata ki se Allah.” Zuciyarta taji ya mugun bugawa ji tayi she can’t proceed with the plans sosai tasan halin Farouq har kasheta ze iya in yagano tricking nasa take, nan tabar maganan zucin. “Ya Farouq na tab’a maka wasa ko k’arya ne? I mean what I said just now.” “Toh Anas fa ya kikeson muyi dashi?” “Ya Farouq muddin baraka rabani da abinda ke cikina ba zan iya sadaukar da son danake wa Anas maka.” Baki ya wage wangalau cike da mamaki. “Fannah kinsan me kike fad’u kuwa? Anas fah? Mr. Fauzi!” “Tabbas nikuwa nasani, Ya Farouq a iya ganinka da banyi ba yau na d’an wani lokaci sena jini incomplete na rasa dalili, dana zauna nayi nazari sena gama soyayya ce Ya Farouq kamar yadda kake sona nima haka nake sonka kawai I failed to notice it ne a da se a yanzu ina fatan am not late zaka karb’i soyayya na.” “Kina sona Fannah? Baki tsaneni ba again?” “Ban tsaneka ba Ya Farouq abu d’aya nakeso agareka kamin shi toh I will be all yours zanyi duk wani abinda ka buk’ace ni.” Baki na b’ari dan jin dad’i yace, “fad’i koma meh Fannah, tell me meh kikeso?” “Karka zubar min da ciki, karka rabani da Baby na kamin wannan ka gama min komai. Shiru yayi na d’an lokaci. “Fannah amman aikema kinsan d’an ba nawa bane cikin Anas ne d’an ze zame mana ciwon idanu a rayuwa.” “Ko kad’an Ya Farouq wannan shine ciki na na farko zanso ace na raine sa nakuma haifar, kaga daga nan kaima se in raini naka cikin ko ba haka ba? Ba kace zamuyi aure ba?” “Tabbas na fad’i haka sede kince baraki aureni ba kinada igiyan auren Anas akanki.” “Ada kenan Ya Farouq, ka kwantar da hankalinka a yanzu haka ban damu da igiyar auren ba ni kawai ka kaini Ukraine dreamland d’ina.” “Amgama wifey zakije Ukraine zakiyi zaman Ukraine achan kuma zakiyi rainon ‘ya‘yanmu.” “Kai amman naji dad’i Ya Farouq toh kud’i fa kanada enough? In babu kayi demanding Anas yamaka sending.” “Eh inada, ina guy daya ara min miliyan biyar d’innan? ba nace miki na miyar masa da kud’in sa ba?” Kai ta gyad’a nufin ta gane. Ya cigaba “toh ai andawo da kud’in d’azu sabida yayi tafiya seko wani sati ya dawo kngga ko kafin wani satin mun tafi Ukraine meaning barin biya sa kud’in nasa ba kenan.” “Are you sure Ya Farouq? Barezo ya kama min kaiba? Kasan banason wani abu ya tab’aminafiyarka.” “Yes wifey kinga yanzu inada miliyan 10 kenan ze ishemu settling a Ukraine.” “Sosai ze isa I really can’t wait so yaushe ne tafiyar? Amman still zanso ace miliyan shabiyar mukeda ina gudun kar goma ya kasa.” “Angama wifey zan kira Anas inche ya dad’o min miliyan biyar.” “You will need my help but.” “Ban fahimce kiba wifey” yayi maganar cikin rashin fahimta. “What I mean is that zaka d’aureni kamar yadda ka saba seka d’aukeni hoto ka masa sending nasan yadda yakesona yana gani na a k’ulle ko miliyan nawa kakeso ze baka.” “Wow wifey wallahi you are a genius!.” “Thank you nace yaushe ne tafiyar namu?” “Bare kai nan da sati ba by God’s grace.” “Okay...” Tace blankly. “So wifey yau zamu kwana tare?” “Don’t rush through Ya Farouq nafison se in munyi aure semu soma had’a kwanciya ka gane?” Kai kawai ya gyad’a “Fannah kalleni.” Idanunta ta d’ago tana kallonsa tare da murmusawa. “Wallahi karki min wasa da hankali I love you amman inhar na gano yo are pranking on me wallahi kinji na rantse ba me iya k’watanki.” “Shikenan Ya Farouq tunda baka yarda dani ba ka sake d’aureni kabani waje, dama ku maza duk haka kuke Anas yak’i kaini Ukraine yanzu kai da kace zaka kainin ma dan kaga inaso kafara corner-corner kaima ba damuwa ka d’aureni ka gudu dani Ukraine amman kasani I will never ever love you.” “Ohh wifey dan Allah karkiyi magana haka I’m sorry kawai I want to be sure ne kuma na tabbata dan Allah karkiyi fushi kinji? Yi hak’uri.” Shiru tayi bata ce komai ba. “Please mana Fannah” ya k’are maganar hannunsa kan nata cike da dabara ta janye hannunta daga nasa “naji amman please karka sake cemin haka zuciyata barata iya d’aukawa ba kasan kalan tashin hankalin dana shiga yau kuwa da bansa wannan kyakkyawar fuskar takan a idanu na ba?” “A’a” ya amsa a takaice yana kad’a kai kamar zombie. Daidai kunnensa ta matso ta rad’a masa wani abu ba tare da tabar wani sassan jikinta ya tab’a nasa ba. Tsabagen dad’in daya ji yayi excusing kansa akan bari yaje ya d’auko mata wani abu yana zuwa. Yana ficewa taja wata doguwar tsuka “Allah ya tsine min ne in fad’a soyayya da azzalimi kamar ka Ya Farouq?” Hannu ta d’aga sama “Ya Allah ka jagoranceni in samu in k’wato ‘yancina k’ark’ashin wannan mugun, Ya Allah kabani sa’an gudanar da wannan plan.” Bada dad’ewa ba yadawo dawani package a hannu “gashi its yours.” “Meshi?” Ta tambaya tana k’ok’arin bud’ewa. Wani had’ad’d’en silver bracelet ne ciki. “Uhm Ya Farouq na waye wannan kuma?” “Naki ne wifey yau nagani a store kawai naji I want you to have it.” “Oh is that so? Thank you” ta miyar ta rufe. “Bara kisa bane?” “Zansa mana, meyesa barinsa ba? Sede Ya Farouq nafison se in munyi aure tukuna in fara sa gifts naka kaji?” “But wifey meh aciki dan kinyi accepting bracelet dana baki.” “Ya Farouq trust me ai yanzun ma nayi accepting zan ajiye a wajena kawai sawane barinyi ba ka gane?” “Nagane wifey muje mu kwanta koh?” “Not yet ka manta zaka tambayai Anas kud’i.” “Ohh haka fa!” Nan ya sake d’ad’d’aureta kamar jiya yayi sending message da pictures d’in wa Anas. Hankalin Anas inyayi dubu be tashi ba ganin pictures na Flowersa d’aure again. ***** “Hello Farouq dan Allah me kakeso? Me kakeso please kadena bata wahala what is you problem?” “My problem? My problem is money kabani kud’i se in sake ta takwanta.” “Jiya jiya fa na maka sending 3 mil be isaba ba?” “Be isa ba dan bance kayi signing sunan FAHNAS enterprises koh? Eh Fahnas enterprise under my name ba shine zaka tsaya kana gaya min magana? Karka turo kaga d’anyen aikin Farouq.” “Wait.. Wait zan turo nawa kakeso please let her go” “Miliyan biyar nake buk’ata.” “Miliyan biyar Farouq?” Ya zaro weak blue eyes nasa. Me ka miyar dani? ATM machine? Kanada ma hankali kuwa? Ko an gaya maka bana calculating millions da nake maka sending ne? Ina zaka kai 15million please?” “Ina ruwanka? Oversabi zaka turo kokuwa inbar matarka ta kwana haka?” “Zan turo son of a b*tch zan turo please ka saketa.” “Inga alert” ding! Ya katse wayar. Bayan minti goma alert ya shigo masa wani shu’umin murmushi ya sakar “Allah sarki d’an amanah.” Bayan ya dawo da kallonsa kan Fannah yace, “stupid d’in har ya turo.” Sosai zuciyarta ke mata k’ona jin yadda hankalin Anas nata ke a tashe “Anas Habeebi very soon in shaa Allah all this will be over more patience please.” Tayi wannan magana a zuci. “Wifey baki jini bane?” Firgit ta dawo reality. “Na’am kace?” “Nace yayi transferring kud’in we good to go now.” “Wow great!” **** “Wifey are you sure zaki iya kwana achan?” Farouq yayi maganar yana miqe kan gado ayayinda Fannah ke maqure bisa 3 seater dake d’akin ta nannad’e jikinta da bargon ruhuwan daya bata. “Yayi Ya Farouq good night.” “Sleep good” anan ya kashe wutar d’akin. _2:57AM_ Bayan ta tabbata Farouq yayi nisa a bacci dan uban minsharin dayake ta rafkawa ta miqe sid’ak sid’ak a hankali tho wutan d’kin a kashene amman kasancewar da akwai hasken moonlight dayashigo ta windown yabata damar ganin duk wan abinda ke cikin d’akin clearly, wajen kansa ta dosa tana taku tsili tsili. Wayarsa ta shiga nema dan texting wa Anas location d’in da take, gefensa ta duba bata ga waya ciki ba. Tunanin koya ajiye wayar k’ark’ashin pillonsa ne ya fad’o mata a rai, farcenta tasoma chi a yayinda take nazarin ya za’ayi ta d’aga pillon nasa ganin ba yadda zatayi ta zaune gefe guda tana me cigaba da tunani chan ta miqa hannunta a hankali takai k’ark’ashin pillon nasa har a yanzu baccinsa yake sha wane wanda ya bugu ko k’ara baiji, lalimar k’ark’ashin pillon tasoma amman takasa jin komai bayan ta tabbata babu achan ta nufo side drawern dake kansa dan dubawa danko jiya ciki taga ya zaro sabon waya. Koya akayi bata lura da glass cup dake gabanta ba oho? K’afanta ya bigesa k’ara ya saki akan tiles d’in adalilin haka Farouq ya miqe zaune. “Way-” be k’are maganar ba yaga Fannah tsaye ganin raba idan da take ba taimakonta zeyi ba ta durk’ushe kawai “awchh!” Tafara faking tana matse babban yatsanta “wayyo Ya Farouq k’afana” wutan d’akin ya kunna sannan ya gwada miqar da ita “a’a karka tab’ani please.” Batasan a lokacinda tayi maganar ba. “Mesa?” Ya tambayeta sounding suspicious. “Uhmm uhmmm I mean karka tab’ani k’afan na min zafi.” “Ohh sorry” a hankali ta miqe takoma kan kujerar ta zauna shima ya zauna a gefenta. “Mugani?” Ya buk’ata. “No karka damu zafin ya ragu.” “Me kika tashi yi da tsakar dare haka? Guduwa kikeson yi komeh?” “Haba Ya Farouq wani erin zance kake haka? Kamar ya guduwa inje ina? Kaima kasan *_INA TARE DA KAI_* ba inda zani wutan d’akin nakeson in kunna...” Tana maganar ta neman inda switch na d’akin ke kar Farouq ya gane k’arya take thankfully taga switch d’in a saman inda side drawer’n yake. “So nake in kunna I want to use the bathroom sekuma na bige k’afa na.” “Next time ki tadani kinji?” “Toh” a hankali ta miqe tasoma k’ingishi “bari ina zuwa” bayi ta nufa tasakar dawani hamdala “Ya Allah nagode daka kub’utar dani daga sharrin Ya Farouq yau. Huh! I have to be very vigilant” bayan data fito suka koma suka kwanta har ayanzu tunanin yazata samu waya take “koda shike baringa zuwa safiya there must be a way!” Se a yau ne tasamu ta kwanta peacefully tun barinta gida. *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:59, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 8⃣5⃣ Asuban fari ta tashi tayi Sallah da nafilfilunta bata damu da tada Farouq ba danko tasan bayi zeyi ba, bayan ta kammala addu’o’inta takoma kan kujera ta zauna tata Azhkar har garin Allah ya waye. K’arfe 8:30AM ta shiga bayi tayi wanka wani highwaist skirt da karinat blue tasa sannan ta lullub’e jikinta da mayafi babba se 9:30AM Farouq ya tashi ”good morning Ya Farouq” ta gaidashi. “Morning wifey how was your night?” “Alhamdulillah I hope yours too, na had’a maka ruwan wanka kashiga kayi semu karya” ba musu ya miqe yashiga anan ta ciro masa wani sky blue jampa ta ajiye kan gadon. Wajen bayin ta nufa ta kasa kunnenta jin bulbulan ruwa ta tabbata wanka yake dan haka ta nufa wajen side drawer’n kansa, kwalin baby nokia sabi tagani har guda biyar wanda taga alamun kamar an bud’e ta k’arisa bud’ewa tacire se juya baya take gudun kar Farouq yafito. Abin takaici taga ba sim ciki ta duba sauran drawers d’inma babu. “Mschww! Ya Salam!” Cikin wardrobe nasa ta nufa tasoma neman sim card one by one take bin kayakin nasa achan counter’n k’arshe taga sim packs kusan goma hamdala ta saki daidai tasa hannu zata zari d’aya kenan Farouq ya murd’a handle na k’ofan, a gigice ta miyar da su ciki. Da towel d’aure a k’ugunsa ya doso inda take “me kikeyi wifey?” Ya tambayeta ba wasa a fuskarsa. B’arin baki ta soma ganin bata gama miyar da kayan nasa yadda ya bari ba. “Uhmm... Ermm. Ya Farouq har ka fito?” “Eh meh kikemin cikin kaya?” “Bbb.. Babu kaga kaya nake nema maka na cire wancan” tayi nuni da jampan dake kan gadon “sekuma bemin ba nafison kasa farin jampa.” “Hakane wifey?” “Eh Ya Farouq fari zefi maka kyau.” Dad’i sosai sokon yaji “toh ai ga inda nake ajiye fararen kayaki na” nan ta matsa masa ya zaro wani farin half jampa “good kayi ka shirya muje mu karya am hungry.” “Okay wifey” cikin d’an k’ank’anin lokaci ya shirya suka fice zuwa dining room achan aka had’a musu had’ad’d’en breakfast suna hira suna chi Fannah na iya k’ok’arinta dan sakewa da Farouq tanason yayi trusting nata sosai. *ANAS* _10:36AM_ Zaune yake a d’akinsa ya had’a uwa uba tagumi gabad’aya ya fita daga hayyacinsa ba aikinsa banda tunanin Fannah rabuwansa da bacci tun da Farouq ya d’auke Fannah. “Anas!” Cewar Abuu yana buga k’ofar d’akinsa. “Kafito mu karya kaji already police d’in suna jiran mu.” Shiruuu... “Anas in shigo?” Nanma shiruu dan haka ya sa kai kawai. Hannu ya dafe a kafad’ar d’ansa. “Anas take it easy wallahi da abinda kakeyi zaka kamu da ciwon zuciya zamu sameta in shaa Allah. Ba kanada bank details nasa ba? Nayi magana da bank d’in za’ayi freezing account nasa.” Cike da tashin hankali ya juyo yana girgiza wa Abuu kai. “A’a Abuu please kar muyi haka wallahi zamu sake worsening situation d’in karmuyi dan Allah banason yayi ma Fannah wani abu.” “Anas wani erin magana kake?” “Abuu please dan Allah kar ayi freezing account nasa ni nasan Farouq.” “Shikenan zan musu magana abari kamar yadda kace yanzu tashi muje mu karya semu fita.” “Abuu fitan nan baida amfani we can’t ever find her hanyan sauk’i shine mu kama Ya Khaleel. yaji an kama Babansa a hannu ze sake min Fannah.” “Anas hakan bame yuwu wa bane we don’t have any evidence da ze nuna Ya Khaleel na aiki da d’ansa.” “Akwai Baba muje mu duba record na Farouq wa yayi bailing nasa am sure Ya Khaleel ne.” “Toh naji yanzu de katashi muje mu karya” Anas ya bud’e baki zeyi magana Abuu ya dakatar dashi “a’a karka cemin bakajin yunwa tashi muje” shida kansa ya miqar da Anas suka nufa dining. ★★★★ *FANNAH* _1:15PM..._ Zaune Fannah da Farouq suke akan dining table daidai zasu fara chin lunch kenan aka k’wank’wasa k’ofa “MB get the door” cewar Farouq kamar yadda ya buk’ata haka MB yayi. “Wayene?” Farouq ya tambayui MB. Kafin MB ya amsa yaron yayi magana; “Bad boy ne ya turoni wai abasa kud’insa.” “Ba yayi tafiya?” Yayi maganar yana barin kan kujerarsa dad’i sosai Fannah taji dataga be d’aga wayar saba, yanzu zata iya texting Anas. Har ya kusan bakin k’ofar sekuma ya dawo ya d’au wayar batasan lokacinda tayi tsaki a fili ba. “Wifey lafiya?” ya tambayeta. “Uhmm lafiya, banji dad’in d’aga kan da akayi bane daidai zamu fara chin abinci.” “Karki damu I will be right back” kai kawai ta gyad’a masa ya fice ya rage daga ita se MB a d’akin, abincinta ta nutsu taci se tunanin ya za’ayi tayi texting Anas location d’inta take. Abu kamar wasa fa Farouq be dawo d’akinba. _32 minutes later..._ K’ofan akayi banging dalilin firgitan da Fannah tayi seda ta yasar da apple dake hannunta tare da juyowa a kid’ime Farouq tagani idanunsa suna wani juyawa kallo d’aya tayi masa tagano abige yake. MB ne ya taimaka ya k’ariso dashi kan kujera ya zaunar dashi. “Omg! Farouq meya sameka haka?” “He had too much to drink” cewar MB. “Okay excuse us zaka iya fita I will take care of him.” Ba musu MB yayi excusing nasu, anitse ta baro kujerarta ta nufa wajensa. “Ya Farouq meya faru? Me kasha haka?” “Karki damu wifey wannan shegen bad boy d’inne yakeson rusa min plans ya dawo kuma yana buqatan kud’insa”. “Toh ka basa mana.” “Wifey kikace miliyan shabiyar kikeso in na basa kud’insa goma ne ze rage.” “Semu sake tambayan Anas ai karka damu kasan me nakeso dakai? Ka huta yanzu kaji?” Kai ya gyad’a mata. Gabansa tayi clearing ta kwantar da kansa a hankali idanunsa suka soma kafewa har bacci yayi gaba dashi. Side pockets na jampan sa ta dudduba bata ga wayarsa ciki ba data leqa setagansa cikin aljihun chest na rigan tunanin ya zatayi ta ciro take seta kai hannunta se tsoro ya hanata danko tana da tabbacin baccin sa beyi nisa ba at any moment ze iya tashi yakamata red handed. Zama tayi gefensa tana tunani chan ta kira sunansa “Ya Farouq!” Shiru ba amsa “Ya Farouq” tad’an buga table d’in. “Urghmmm” yayi groaning cikin bacci. “Ya Farouq ka tashi muje d’aki ka kwanta kaji? Nan is uncomfortable.” “Bari karki damu.” “Dole in damu mana Ya Farouq d’ina na kwance a tak’ure tashi muje d’aki kaji?” A kasalance ya miqe dan yadda ya bugu ko bud’e idanunsa bai iyawa dan bata da wani hali ne kawai tasa hannu ta taresa ganin yakusa fad’i a k’asa. “Astaghfirullah” ta rigayi har seda ta jibgesa kan gadon d’akinsu. Kamar mamaci ya soma sabon bacci wajen. Bad to worse tace a ranta “yanzu ya zanyi inciro wayar yadda yayi ruf da cikin nan?” dabara ce ta fad’o mata. “Ya Farouq ka cire kayan mana zaka fi jin dad’in baccin...” Shiruuu “Kaji Ya Farouq tashi ka cire kayan se ka kwanta” da k’yar ya tashi ya cire kayan ya wurga mata hamdala ta saki. “Rataya min akan drawer” yayi maganan a bige. Yadda ya buk’aceta tayi a hankali ta juyo ta kallesa ganin idanunsa a rufe tasoma lalimo aljihun nasa dan ciro wayar har takai kai sauran cirewa kawaibFarouq ya miqe, da wuri tabar wajen ta k’ariso wajen gadon “mene ne Ya Farouq?” Bakinsa kawai ya toshe agurguje ya ruga bayi amai ya riga kwararowa hakan yabata daman ciro wayar, b’ari duk wani sassan jikinta ke har tasamu tayi texting Anas kamar haka; _Anas Habeebi its me Fannah, Mobil filling station Yobe by pass come ASAP and save me please PS don’t call._ Bayan tayi sending tayi deleting a take, kafin tace zata miyar da wayan Ya Farouq ya fito daga bayin idanunsa basu sauk’a ako ina ba se Fannah dake riqe da wayansa seda ya k’ariso gabanta ya tambayeta “meh kike min da waya?” Gabaki d’aya ta tsure kasa koda furta ‘A’ tayi se rawa jikinta ke. “Magana nake miki meh kikemin da waya?” “Bbb... Babbu..” Hannu yasa ya fisge wayar, call logs ya shiga ya duba sannan messages nanma bega wani abu ba sede jikinsa na basa ba lafiya ba. “Baki amsani ba nace me kikemin da waya?” “Bb... Babu Ya Farouq wayar ne ya fad’i garin rataya maka kayan naka shine na d’ago.” Tayi magana cikin murya me rawa. “K’arya kike Fannah meh kika min da waya?” “Allah babu Ya Farouq ka duba kaga.” “Fannah kinsan in na gano wasamin da hankali kike zan mugun sab’a miki.” “Ya Farouq ya kake magana haka ne? Kaima kasan wannan ba trick bane inasonka Ya Farouq.” “Barin ga ko dagaske ne kinaso na.” GPS radio yayi turning off sannan ya kira Anas*** *ANAS* Yana cikin motarsa acikin gari yanzu barinsa police station an yarda da yamma za’a je a duba record na Farouq. Driving yake a hankali koda yaji wayansa yayi k’aran shigowan new message a while ago be damu yaduba ba acewarsa seya isa gida ya duban. Ganin kiransa kuma ake yanzu ya d’ago wayar ya duba sabon layi yagani kafin ya nemi waje yayi parking ya d’aga wayar ya tsinke. Daidai zeyi calling back kenan yace bari ya duba saqon tukunah. K’wararo idanunsa waje yayi bayan daya karanta. “Flower! Its Flower!” Har ya danna numban ze kira sekuma yatuna tace kar ya kirata take yayi mastering numban kar incase zata kirasa. Yakai kan numban Abuu kenan yaga exact numban da Fannah ta turo masa message dashi na kira, ba tare da b’ata lokaci ba ya d’aga “hello Flower??” Wani shu’umin murmushi Farouq ya saki yana kallon Fannah “so its true you called him with my number koh?” kafin ta hankara ya shaqure mata wuya hannunsa tahau bugi “Ya Farouq dan Allah kayi hak’uri ka sak.” Kasa k’arisa maganan tayi dan yadda ya shaqe mata wuya. “Hello Farouq?! Me kake mata please ka saketa. Flower kina jina?” “Anas Habeebi please help me ze kasheni.” tayi maganar da k’yar. “Farouq me kake mata? Ka saketa please dan Allah don’t hurt her.” “Kasheta zanyi ni zata raina ma wayo kasani kayi ban kwana da matarka dakuma d’anka” yana kaiwa nan ya katse wayar. Koda Anas ya sake gwada kira kuwa bai shiga Abuu ya kira da sauri ya fad’a masa location da Fannah ke, shima Abuu ba tare da b’ata lokaci ba ya sanar da police koda ya cewa Anas ya jira sutafi duka a tare k’i Anas yayi he can’t wait to save his Flower. **** “Kiransa kikayi ko meh? Munafukar Allah kawai ni zaki raina ma wayo kiyi tricking d’ina? Me kika yi da wayan nache?” “Aahh..hahhh” ta soma wani erin nishi. “Yya.. Farouq dan-” sama sama nishinta ya soma ganin zata mutu masa ya saketa tari ta hau yi idanunta sun kad’a sunyi jazir suna tsiyayar hawaye. “Wait what do you mean da kikace Anas yazo ya taimakeki, texting masa location d’innan kikayi? Magana nake miki!” Nanma shiru se tari take tayi. “Kin fad’a masa location da muke koh? Hohoho! Smart girl zakiyi bayani.” Akwati ya ciro yasoma had’a musu kayakinsu har a yanxu Fannah bata yi recovering ba daga shaqentan da Farouq yayi bayan yagama had’a musu kayakin ya tattara abubuwan daze buk’ata “tashi mutafi.” “Ya Farouq dan Allah kayi hak’uri karka kaini wani wajen.” “Maganan banza ina ni zaki raina ma wayo? Semuga ya Anas nakin ze cetoh ki” bejira ta sake cewa wani abu b ya fisgota sannan ya soma janta se rok’onsa take amman ko a kwalan rigarsa. Daidai wajen staircase ta durk’ushe ta kankame k‘arafun “meh haka?! Ki tashi mutafi.” “Wallahi barin bika ba mugu kawai ka sakeni.” “Ina wasa dake ne?! Nace ki tashi!” sam tak’i motsawa ganin ba mahalicci se Allah ya sauk’a ya ajiye jakan nasu sannan ya sake haurowa nan suka shiga dambe sam tak’i sake k’arafun gagam ta rik’e ita barata bisa ba seda yayi dagaske sannan ya samu ya sauk’o da ita se fad’anshi take. Wani syrup ya ciro daga cikin jakar. “Ya Farouq dan Allah kayi hak’uri karka sani shan wannan abun, na tuba dan Allah kayi hak’uri...” Ko sauraranta beyi ba yaja hannunta ya danne ta a k’asa tare da had’a hannayenta biyu gu d’aya, kwalban yakai mata baki sede sam tak’i bud’ewa “ki bud’e nace!” Se hawaye take abin tausayi tana girgiza masa kai, “nace ki bud’e” goshi ya gara musu wanda sanadin haka ta bud’e bakinta tare da sakar dawani irin azabartacciyar k’ara, hakan yabasa daman sa mata kwalban a baki seda ya juye mata tas sannan Ya cire, tarawa tayi a bakin nata tak’i had’iyewa “ki had’iye nace!” ganin tak’i had’iyewan kuma tana cinye masa lokaci ya matse mata hanci tun tana iya jurewa har numfashinta ya soma yankewa idanunta sunkad’a sunyi wani irin jaa bayan riqe numfashinta data tayi daga k’arshe kawai ta had’iye ganin zata iya mutuwa ga mugun yak’i sake mata hanci kuma. Daidai nan aka hankad’o entrance door d’in da wani irin force da seda ya k’ofar ya fad’i a k’asa da hanzari Farouq da Fannah ke kwance bisa cinyansa idanunta suna wani kakkafewa ya miyar da kallonsa bakin k’ofar. Fannah kuwa da k’yar idanunta suka iya comprehending mutumin dake tsaye bakin k’ofar. “Anas! Habeebi” kad’ai bakinta ya iya furtawa. “FANNAAAHHH!!!” Ya kira sunanta cikin tattausar murya me uban sauti. Sandarewa Farouq yayi wajen yarasa taya Anas ya samu ya shigo bayan uban securities daya zuba awaje be k’arisa wannan nazari ba yaji an cukumo mai collar riga. Kafin ya hankara Anas yakai masa wani erin mumunar punch da hannunsa me zobuna uku, take hancin Farouq ya fashe ya soma zuban jini. Wani punch d’in ya sake kai masa aciki tare da miqar dashi ko ta kan Fannah beyi ba, nishi yake tamkar zaki. Dogayen k‘afafunsa ya d’aga d’aya ya tunkud’e Farouq dashi seda yayi tumbling a k’asa Anas be barsa ba ba har yanzu. Sleeves nasa ya sake rolling yabi kan Farouq tareda hayewa kansa yasoma kai masa punches tako ina afuska ko wani spot a fuskan Farouq zuban jini yake har yanzu Anas be barsa ba seda yaji muryar Fannah tana kiransa. “Anassss!!!” Da ihu, alokaci guda ya bar abinda yake tare da kewayo wa. “Anas please help me, wayyo Allah !!” ta k’are maganan hannunta dafe kan cikinta se juyi take a k’asan ga wani erin azaban da ita kad’ai tasan yadda takeji acikinta. Hawaye take me tsuma zuciya. A gurguje Anas yayi kanta tare da aza kanta kan cinyansa. Hannunsu ya had’e “shhh! Flower am here, your Habeebi is here kinji stop crying.” A kasalance ta d’ago idanunta ta azasu kan fuskarsa daba abinda ke kwance akai banda tsantsan damuwa da tashin hankali a raunane. “Habeebi I’m sorry, I‘m sorry plea-” bata k’are maganar ba ta sakar dawai irin wahalallen k’ara; “Arghhh! wayyyooo Alllahh cikina Anas help me please zan mutu wayyyooo Allah!!” ta k’are maganar hannunta dafe kan cikinta. “Flower me Farouq ya miki? Meya miki?” Yayi maganar cike da tashin hankali. Da k’yar ta iya nuna masa kwalban da yatsanta, a hanzarce ya miqa hannu ya d’aga “Nooo!! Nooo!! Nooo!! please” abinda yake ta furtawa kenan bayan ya karance jikin kwalban, wani irin k’ara Fannah ta sake sakarwa tuni ya jefar da kwalban tare da d’aga skirt nata jini yaga yana bin k’afafunta unstoppingly. “Noo!! please NOOO! Fannah please noo Flower.” “Anas I’m sorry ple-” bata samu daman k’arisa maganan ba idanunta suka ruhu ta bar motsi kwata kwata. “Flower I can’t lose you please wake up dan Allah kitashi please Flower I can’t leave without you, don’t leave me please” jinin dake bin k’afafunta se dad’a yawa yake. Rungumota yayi a jikinsa gagam tare da had’a musu goshi se kuka yake yana sunbatu. Daga bisani ya mik’e a fusace ya nufi kan Farouq da har ayanzu ya kasa koda motsa k‘afa dan yadda ya bugu kansa Anas ya haye tare da shaqure masa wuya da k’arfin da Allah ya basa, zuciyansa se tafasa yake yana saqa masa ya kashe Farouq kar yayi sparing nasa. “You must die you filthy son of b*tch you are going straight to hell...” *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:59, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 8⃣6⃣ Take idanun d’an banza da sukaji rauni suka kad’a sukayi wani irin jaaa, hannayensa biyu na akan hannun Mr. Fauzi dake wuyansa yanata k’ok’arin cire hannayen amman ko kad’an yakasa dan bayida k’arfi ko kad’an Anas ya riga ya masa liqis. “An.. An... Anas ple...” Tari yafi k’arfinsa har anan Anas yak’i sakesa as ya d’au alwashin seya kashesa. Wani irin nishi Farouq yasoma ja da k’arfin bala’i. “ANAASSSSS!!!!” yajiyo muryan Abuu from far. “Anas don’t kill him ka sakeshi” yayi maganar yana gudu har seda ya iso wajen, k’ok’arin jan Anas daga kan Farouq yake amman ya kasa, “Anas ka sakeshi karka kashesa” seda wasu police guda biyu suka sa hannu sannan aka samu aka d’aga Anas daga kan Farouq. “Noo kubarni in kashe bastard d’innan, he dsereves nothing than to die. Let me go! Ku sakeni!” turesu gabad’aya yayi harda Abuu sannan ya sake komawa kan Farouq yakuma shaqure masa wuyan again, tsantsan azaba k’afafun Farouq se dancing suke, sake binsa su Abuu sukayi sunata k’ok’arin d’ago Anas har a yanzu Abuu bega Fannah ba se da ya juya kansa yaganta kwance so lifeless a k’asa gakuma jinin dake ta fitowa daga jikinta har yanzu. “Fannah!!” Ya kira sunanta da k’arfi hakan yasa Anas dawo da kallonsa wajen shima. “Anas ka sake Farouq its Fannah you need to focus on Anas matarka!” Da k’yar suka d’aga shi, da gudu yayi kan Fannah ya tattara ta a hannunsa se cikin motarsa a yayinda Abuu ya tsaya da police d’in ana carrying investigations, jakan kud’i da komai da komai duk aka sa cikin motar police daga k’arshe Farouq aka d’aga shima aka kaisa asibiti dan ko bara a iya hukuntasa a haka ba dole se ya samu sauk’i. _An hour later..._ Baba, Mami, Afrah, Aiman, Abuu, Anas, Ummie, Shettima dakuma Amal duk zaune suke a harabar d’akin Fannah dukkaninsu fuskokinsu cike da damuwa, daga masu kuka se wanda suka had’a tagumi babu kaman Anas da ya kasa zama gu d’aya se pacing yake. Abuu ne ya miqe ya nufa inda Anas keta jeka ka kadawo tare da dafe kafad’ansa. “Anas you need to calm down in shaa Allah Fannah zata samu sauk’i muna nan muna mata addu’a taho muje ka zauna.” “Abuu I can’t wallahi in wani abu ya sami Fannah ko abinda ke cikinta I must kill Farouq with my own hands.” “Kabar magana haka in shaa Allah ma ba abinda ze samu Fannah” ya kwanto da Anas jikinsa yana bubbuga bayansa a sannu sannu yaja Anas suka koma suka zauna. Hannu yasa ya share hawayensa “Abuu mesa za’a kawo wancan son of a b*tch d’in nan asibitin? Mesa basu kaisa wani asibitin ba? Abuu why? Infact bekamata ma akawosa asibiti ba compared to abinda yama Fannah.” “Anas muyi focussing akan Fannah yanzu Farouq will follow afterwards.” _5 minutes later..._ Red globe dake a saman k’ofan d’akin da Fannah ke ciki ne ya d’auke in some seconds k’ofan ya bud’u atare duka families d’in sukayi wajen Anas ne a gaba. Cike da tashin hankali yake maganar “D... Dr... Dr how is she? How is my wife?” Ganin yadda Anas ke cikin tashin hankali Dr’n ya dafesa a kafad’a “Mr. Fauzi calm down karka damu your wife’s condition is stable zaka iya shiga ganinta bayan nan duka family zasu iya shiga ganinta also.” “Alhamdulillah! Dr. What of the baby? Shima ya rayu? Were you able to save my baby?” Kai kawai ya iya ya girgiza masa. “No Dr dan Allah karkace kun kasa saving babyna please...” ya k’are maganar cikin sautin kuka. “I’m so sorry Mr. Fauzi there is nothing we could do saboda anriga anyi terminating cikin ba yadda za’a iya saving baby’n it was destroyed already tun kafin kuzo nan, maganin Misoprostol da aka bata yagama aiki, maganin nada k’arfi sosai and yana leading to hard and painfull miscarriage we should be thankful ma maganin be b’ata mata hanji ba saboda overdose da aka bata.” “Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un” kad’ai ke tashi awajen se kuma sautin kukan da yabiyo baya Mami nayi Baba bata hak’uri haka Ummie da Amal ma, Afrah kuwa Shettima ne ke condoling nata. “I’m sorry excuse me please” yana kaiwa nan ya fice. Anas kuwa kasa riqesa k’afafun sa sukayi suuul ya sulale k’asa da wuri Abuu ya sake Ummie ya tarosa. “Ya kashe min baby Abuu he murdered my child.” “Shhh! Anas kayi hak’uri” A fusace ya miqe Abuu da Shettima suka soma kiran sunansa suna binsa, gudu yasa be tsaya ko ina ba se a d’akin Farouq. Banging k’ofar yayi take Ya Khaleel dake zaune gefen Farouq da kayinsa duk bandage hannunsa kuwa handcuff ne had’e da gadon dayake kwance akai. Kamar a kyaftawan ido Anas ya had’e Ya Khaleel da jikin bango tare da shaqure masa wuya Abuu da Shettima ne suka shigo da wuri suna k’ok’arin karb’e Ya Khaleel amman sun kasa dan yadda Anas ya rik’esa. “Ina kaga abinda shegen d’anka yayi wa Fannah? Kagani koh? And you are the one responsible irresponsible father kawai, wallahi both of you must pay.” da k’yar Ya Khaleel ke maganan “Anas dan Allah ka sakemin wuya dan-” tari ne yafi k’arfinsa da k’yar da taimakon wasu doctors biyu aka k’wata Ya Khaleel se shafa wuyansa daidai inda Anas ya kama yake idanunsa sunyi wuru-wuru. Kamar me aljanu Anas yayi kan Farouq da rai ke a hanun Allah ya shaqe masa wuya shima da wuri aka k’wato sa. “Anas get your senses kowa yasan abinda suka maka da zafi amman in ka kashe Farouq yanzu babban matsala ne a garemu, kotu ne zasu hukunta Farouq bamu ba.” “Nasani sede kafin nan inason inbawa d’an banza kashi” nan yasake yin kan Farouq sede kafin yamasa wani abun aka taresa. Cikin wani irin sauti Farouq ya soma magana “duk kaine Baba wallahi duk kaine barin bari akaini prison ni kad’ai ba.” “Meh kake cewa haka Farouq?” Cewar Ya Khaleel cikin rud’ani yana matsowa kusa da Farouq gudun kar ya tona masa asiri. “Aikasan me nake nufi, da tun farko baka fiddoni daga prison d’inba daduk haka be faru ba.” “So its true!” Cewar Anas “I knew it dama ai na fad’a maka Abuu wannan” ya nuna Ya Khaleel da yatsa “munafiki ne, zakusan no one messes with Mr. Fauzi or his property, musamman kai Farouq” yanuna sa da yatsa “Shariah Court zankai ka su yanke maka hukuncin kisan kai kamar yadda kayi murdering min baby kaikuma uban banza sena tabbata an yanke maka shekaru da dama a gidan yari anan ne zan iya samun peace of mind.” Wani wawan dariya Farouq ya b’arke da, “ko a babu nasan na rabaka da source of happiness naka.” Daidai Anas zeyi kansa dan kai masa punch su Abuu suka riqesa “lets go Anas mu fita kaje ka duba Fannah kabar nan” da k’yar aka samu aka fiddo shi daga d’akin. **** A hankali ya bud’e k’ofan d’akin da Fannah ke ciki. Kwance yaganta bisa gado abin tausayi, besan a lokacinda idanunsa suka cike da hawaye ba if only ze iya amsan rashin lafiyan da yayi, ina ma ace ze iya karb’an duk wani pain da takeji right now da yayi. Kujera ya matso dashi kusa da gadon nata tare da zama. Ko hannunta yakasa riqewa dan tausayi, hawaye yake sosai a hankali ya d’aga hannunta ya had’a da nasa tare da pecking hannun. Da alama bacci take dan kuwa bata bud’e ido ba har a yanzu. D’ayan hannunsa yakai kanta yana shafa uban gashin dake kwancd akan goshinta, ya d’au tsawan minti uku yana ahaka sannan a hankali Fannah tasoma bud’e idanunta har ta bud’esu duka. “Habeebi” tace cikin dashasshiyar muryarta duk yadda yayi dan stopping hawayen nasa ya kasa kai ya miqa yayi pecking nata a goshi. “Flower welcome back” yayi maganar yana mata murmushi itama murmushin ta miyar masa a wahalance. Data gwada zama kuwa sam takasa dan zafin da takeji daga k’asan mararta, wani irin wahalallen k’ara ta saki da sauri ya sake kwantar da ita. “Not yet Flower don’t move kinji? am here sweetheart” ya sake pecking nata a goshi. “Habeebi mesa kake kuka?” Tayi maganar idanunta na cikowa. “Babu, am just happy you are back baki tafi kin barni ba, Flower I love you so very much” ya matse hannunta cikin nasa. “I love you so much more Habeebi barin tab’a barinka in shaa Allah.” “I know Flower nasan baraki barni ba I was just scared.” Yasa hannu ya share mata hawayenta “karkiyi kuka kinji? Its bad for your condition.” Kai ta gyad’a mai, “Habeebi what of our baby? Yana nan?” Ta tab’a kan cikin nata tana shafawa a hankali. Shiruu Anas yayi danko besan ta ina ze fara mata bayani ba. “Habeebi mesa kayi shiru? please tell me baby na nanan kokuwa ya tafi?” Nanma shiru kuka ta soma sosai “Habeebi kafad’amin please, tell me my baby is still with me, tell me burin Ya Farouq na rabani da baby na be cika ba please Habeebi.” “Shhhh!” Ya aza yatsansa kan lips nata “bar kuka kinji?” Ya share mata hawaye. “Habeebi please tell me” seda yayi kissing forehead nata sannan yace, “Flower ki kwantar da hankalinki kinji? I’m so sorry nayi delaying time, da a lokacin da kika turo min da saqon nazo dana hana aukuwan wannan abu, am sorry please.” Maganansa ya tabbatar mata ta rasa babynta. “Habeebi so the baby is gone?” Ta tambayesa. “Ka fad’a min please.” Cikin wani erin salo ya gyad’a mata kai “baby ya tafi ya barmu Flower, we’ve lost our baby all because of me, I’m sorry.” “Habeebi ba laifinka bane laifi na ne, da ban had’iye maganin ba da babynmu be tafi ya barmu ba, ni na kashe babynmu da kaina...” ta rushe da kuka. “Shhh!” yasa hannu yana share mata hawaye “don’t ever talk like that Flower ba laifinki bane, mugodewa Allah you are back, mugodewa Allah Farouq be samu ya kaiki wani wajenba in shaa Allah, Allah ze kawo mana wani baby kinji? Kibar kuka and I promise you Farouq will come nowhere near you again ko fuskarki bare sake kalla ba.” Kai ta gyad’a masa cikin kuka yana share mata hawaye seda ya tabbata tayi shiru ya kirawo su Abuu da su Baba duk suka shigo suka gaishe da Fannah. ★★★★ Tun daga nan aka soma jinyan Fannah, sosai take samun kulawa gun Maminta, Ummie ma kusan a asibitin take yini se dare take tafiya haka Anas ma kullum yana gefen Fannarsa yana bata iya kulawan daze iya, office gabad’aya yabar zuwa yabar Kacallah in charge. Kamar yadda yayi promising kuwa seda ya cika, Shariah court yakai Farouq inda achan aka yanke masa hukuncin rataya na kisan kai dayayi, kafin nan Abuu yace inhar Farouq ze bawa Anas hak’uri yanemi gafararsa za’a janye zancen amman ina Farouq taurin kai wane tsohon k’adangare yace ya gommaci ya mutu daya bawa Anas hak’uri haka a idan mutane aka mai rataya ya wuce lahira. Ya Khaleel kuwa 10 years imprisonment aka basa na bada goyin bayan kisan kai da yayi, daga nan aka rufe chapter’n Farouq da Ya Khaleel. *(NOTE: ga masu fad’in kar a hukunta Farouq kusani hukunci ne me tsauri wato kisan kai ya dace dashi saboda yayi aborting baby wanda yake daidai da committing murder, inkuma har wai ba kashesa akayi ba aka yanka masa wasu shekaru a gidan yari toh definately wata rana ze fito kuma ze cigaba da hunting Fannah)* ***** _1:05PM_ A yau aka sallami Fannah daga asibiti sosai Dr yabasu shawarwari ciki harda hutun ‘yan watanni da Fannah ke nema kafin ta sake d’aukan wani cikin. Bayan isowansu gida Fannah taga security men as in k’warraru designed security men guda biyar bakin k’ofar. “Habeebi wannan mutane fah?” “Your security men Flower in shaa Allah from now no harm will come to you.” “Habeebi ai dama enemy d’in d’aya ne Farouq kuma he is gone yanzu ba me sake tak’ura mana.” “Even still Flower I want to keep you safe, ban tunanin zan iya yafe wa kaina in wani abu ya sake samunki, you are a like Flower da ba’ason abinda ze tab’a sa” murmushi ta saki masa, bayan yashigo yayi parking motar sannan ya ciro luggages natan yayi ciki dasu, da kansa ya cirota daga motar yakaita har d’akinsu. “Thank you Habeebi.” “Always Flower” yayi maganar yana ciro mata towel nata daga wardrobe “gashi kiyi wanka semuci abinci I cooked your favorite.” “Favorite wanne kenan? louisiana?” “Yes sweetheart kishiga kiyi wanka ko in miki?” Towel d’in ta fisga daga riqonsa “haka kawai seka haumin wanka?” “Barin iya bane?” “Eh” ta fad’a tare da murgud’a mai baki. Gabanta yasha tare da d’agata sama chak! be direta ko inaba se cikin jacuzzi sannan yasoma raba ta da kayan jikinta. “A’a Habeebi wallahi zaka iya kayi hak’uri kabari please.” “LOL shegen kunyan kinnan bansan ranan barinsa ba, ina jiranki” nan ya manna mata peck a kumatu sannan ya fice. Cikin kwanciyan hankali ta samu tayi wankanta ta fito zaune ta tarar da Anas gefensa wani baggi T shirt ne baby pink in color da hoton birds da flowers akai. “Come here” ya buk’ace ta, ba gardama taje ta zauna gefensa, akan cinyansa ya azata sannan yaciro lotion nata ya soma shafa mata sam bata hanasa ba bayan da yagama takallesa cike da so da k’auna tana murmushi sannan tace, “thank you Habeebi.” “Its my job Flower in tayaki sa kayan?” “A’a karka damu” a hankali tasa kayan daya cire mata wanda tsayin yamata daidai tsakiyar cinya. “Toh Habeebi ba leggings da zan sa taciki?” “Babu I missed your sexy legs so yau inason inta kallonsu.” “LOL” ta murmusa “baraka kasheni da kayan dariya ba Habeebi toh muje muci abincin” tayi maganan tana bin jikinta da turare bayan tagama ya rik’o hannunta suka fice daidai gaban d’akin babynsu ta tsaya hakan yasa Anas tambayarta ko lafiya. “Flower wani abu ne?” “Habeebi kawai na tuna da babynmu ne, I miss him/her” ta k’are maganar tare da aza hannunta kan cikin nata. Ganin zata fara masa kuka yayi sauri yayi hugging nata yana bubbuga bayanta. “Is okay Flower Allah ze kawo mana wasu in shaa Allah bar kuka kinji?” Hannayenta ta zagaye a bayansa a hankali tana gyad’a kai “I pray so Habeebi.” Sun d’au minti biyu suna manne da juna sannan Anas ya raba jikinsa da nata “muje muci abincin ko? Se kisha meds naki” “Yes amman inason inshiga d’akin first.” “A’a Flower banason kiyi kuka kuma nasan definately kika shiga zakiyi.” “Please Habeebi” badan yanaso ba yabud’e masu k’ofan suka shiga. Daidai gaban babban gadon ta tsaya tare da sunkuyawa ta ciro d’aya daga cikin cute pink teddy bears d’in tana murmusawa, hawaye kawai tasoma zubarwa, kafin tasa hannu ta share Anas ya riga ya ganta. “Flower kinga shiyasa nace banason kishigo.” “Habeebi ka tuna lokacin da nace mu sayi blue ones kace a’a pink kafiso saboda jikinka na baka mace zamu haifa? Kasan wani name ya fad’o min alokacin?” “No Flower tell me” ya juyo da ita gabansa tare da kwantar da kanta a chest nasa yana shafa bayanta. Kanta ta d’ago tana kallonsa *“HANAN* Habeebi. Kasancewar kanason baby girl nima na soma ji ajikina mace zan haifa and *HANAN* zanso muna kiranta dashi amman not anymore Habeebi...” sekuma ta rushe da kuka. Face nata yayi cupping yana share mata hawayen “kibar kuka kinji sweetheart? We will have another baby and many more kuma aduk lokacinda muka samu baby girl I promise you ke da kanki zakiyi naming nata *HANAN* kinji? Bar kuka.” Kai ta gyad’a a hankali tare da hugging nasa gagam a jikinta. “I love you Habeebi, I love you so much.” “I love you too Flower muje muci abinci.” Teddyn ya amsa ya ajiye sannan ya jata har a yanzu bata bar kukan ba, shida kansa yake bata abincin har ta k’oshi sannan ya b’allo mata meds nata ya bata bayan sun idar da Sallah suka fita waje garden dan shaqatawa kan wani dogon kujera suka zauna ya kwantar da ita ajikinsa me bala’in sata mance da dukkannin damuwanta. Hannu yasa cikin ¾ wandonsa yaciro wani heart-shaped pack tare da miqa mata. “Habeebi meh wannan?” “Its yours bud’e kiga.” Excitedly ta amsa ta bud’e had’ad’d’en silver bracelet taga aciki meh chain d’an dogo seda toliyar heart a k’arshen wanda yake nan d’an babba. “Wowww its a beauty!” tayi exclaiming. “Do you like it?” “I love it Habeebi.” Hannu yasa ya ciro daga pack d’in tare da d’ago siririn hannunta ya sa mata chas ya zauna. “Just as I imagined it” ya fad’a tare da kissing hannun nata. “Tsaya kiga wani abu.” Toliyan heart d’in ya bud’e mata _“FAHNAS”_ taga rubuce ciki in italics. “Habeebi this is way beautiful” fuskarsa ta riqo tayi pressing masa appreciating kiss daya kashe masa jiki lokaci guda, koda ta gwada sakesa kuwa holding lips natan yayi ya cigaba da kissing nata seda suka ji kansu problem free sannan ya saketa, murmushi ta sakar masa “I love you my sugar lips.” Murmushin shima ya miyar mata “sugar lips?” Yayi maganar da gira d’aya a d’age “ofcourse Habeebi I missed your lips and your body” kafin ya hankara ta sake pressing masa another hot kiss, se kissing juna suke passionately and hungrily tamkar yau suka fara tasting juna**** _some minutes afterwards..._ “I love you Flower.” yace da ita yana shafa dogon sumarta. Sake shigewa jikinsa tayi; “And I love you too Habeebi like bohot bohot!” ta sakar masa da best smile nata me mugun amsar ta dakuma birkita wa Anas lisafi. *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:59, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 8⃣7⃣ “Yauwa Habeebi nace ya labarin Moosa ne? Har yanzu shiru ba’a samesa ba?” yatsunsu yayi interwining; “D’azu munyi magana da police sunce suna kan investigating har yanzu, kinsan Farouq shege ne Allah kad’ai yasan inda yakaisa.” “Allah sa a samesa a raye Habeebi nasan danni Ya Farouq ya masa duka haka saboda yak’i shigo dashi ciki.” “You are right Flower in shaa Allah zamu sam-” besamu daman k’arisa maganan ba sakamakon ringing da wayar sa yasoma ganin number’n Inspector General yayi saurin d’agawa. “Hello Inspector.” “Yes Mr. Fauzi I will like to congratulate you.” “Yes... About what Sir?” Yayi maganar cike da neman k’arin bayani. “Mun samu Moosa your driver achan Mongunu wai gidan Bad Boy achan Farouq ya kaisa ya b’oyesa.” “Alhamdulillah, Alhamdulillah this is indeed a great news.” “It is kuma shima Bad Boy d’in yana a hannu yanzu according to record babban drug dealer ne partner in crime na Farouq kuma dan da miliyan biyar nasa akayi bailing Farouq a prison 2 weeks ago.” “Okay... Thank you Sir ina Moosan yake yanzu?” “An kaishi asibiti dan duba lafiyarsa I guarantee you ba abinda suka masa.” “Ina godia Sir zamuyi magana anjima.” Nan ya katse wayar tare da juyo da kallonsa kan Fannah dake kallonsa fuskarta d’auke da tambaya. Kafin tayi magana ya aza yatsansa kan lips nata “nasan me kikeson tambaya, an samu Moosa? Ko ba haka ba?” “LOL eh haka please an samesa?” “Yes sweetheart an sami Moosa yana asibiti yanzu as we speak yakamata inje in duba sa, I will be right back.” peck ya manna mata a goshi kafin ya miqe ta riqo shirt nasa. “Habeebi nima zanje.” “Zakije ina?” ya tambayeta disbelievingly. “Asibitin mana nima in duba sa kasan fa nice sila.” Kai ya kad’a mata “inaaa! you are going nowhere ko kin manta kema yau aka sallamoki? Bafa kida lafiya ki zauna ki huta barin d’au lokaci ba zan dawo kinji Flower?” “O’o” ta shakwab’e fuska. “Flower please kiyi hak’uri ki zauna zan isar masa da saqon gaisuwanki bareyi ki bini ba.” Badan tana so ba ta gyad’a kai wearing a sad face. “Flower ba goodluck kiss?” “Eh babu” ta fad’a ba tare da ta kallesa ba. “Oh common! Flower.” Alokaci d’aya ta d’ago fuskarta tana mai murmushi “Habeebi na gabad’aya ze fita barin basa goodluck kiss ba? Impossible!” a hankali ta had’a musu lips tare da kissing nasa a passionately. “Off you go take care okay?” “I will and you too Flower, in shiga dake ciki ko zaki iya?” “Don’t bother zan iya I love you” “I love you too Flower.” har ya soma tafiya ta tsayar dashi “wait wait tsaya in d’aukemu selfie so I can be starring at my husband’s handsome face kafin ka dawo.” Murmushin jin dad’i ya saki tare da dawowa baya ta d’aukesu sannan ya fice, anan yashiga ya fito da key’nsa ya fice itama bada jimawa ba tashiga ciki. *****_3:10PM_ Daidai nan Anas ya dawo gida rashin ganinta a parlour ya tabbatar masa a d’aki take aiko yana shiga d’akinsu ya sameta zaune kan dressing mirror se sosa cikin gashinta take da comb tsantsan k’aik’ayi. “Flower” ya kira sunanta anan ne tasan da shigowarsa ta juyo tana kallonsa cike da so da k’auna “sannu dazuwa Habeebi.” “Thank you, me kikeyi haka?” “Wallahi kaina k’aik’ayi na kwana biyu ban wanke ba, ya jikin Moosa’n?” “He is okay alhamdulillah.” Yayi maganan yana dosowa gabanta. “Toh masha Allah, aha! Mami ma ta kira tana gaisheka” tacigaba da sosa cikin gashintan. “Ina amsawa” yace tare da karb’e comb d’in daga hannunta. “Habeebi bani please k’aik’ayi” ajiyewa yayi kan mirron tare da rik’o hannunta “muje in wanke miki kan Flower.” Dariya sosai ta tsaya yi wanda sakamakon haka Anas ya tsaya kallonta yana admiring nata, dariyan sa na mugun kashesa. “Habeebi baraka isheni da kayan dariya ba, yaushe kazamo hair dresser da zaka wanke min kai?” “Aww bakisani ba Flower? I can be anything fo you, Dr, hair dresser, cooku, servant komi da komi ma, muje.” “A’a please kabari.” “Flower banason dogon surutu” hannunta ya sake ya shiga cikin wardrobe ya ciro mata vest tare da miqa mata “sa muje in wanke miki” anan shima ya rage kayan jikinsa ya ragar da singlet se ¾ wando zallah. Ba musu ta cire T- shirt d’in tasa vest daya kawo mata acikin jacuzzi ta zauna ya karkato da kanta direction guda. “Welcome to FAHNAS beauty salon how can I help you Mrs. Fauzi?” Dariya sosai take “thank you, wash and set nakeso.” “You are at our service.” Daga farko seda yayi combing dogon sumanta sannan ya wanke thoroughly da ruwa sekuma da shampoo, a hankali yake mata massaging kan wanda ke mata dad’i sosai cikin d’ank’ank’anin lokaci ta nemi k’aik’ayin ta rasa. Bayan daya gama wanke mata ya d’aure mata kan da towel sannan ya miqa mata babban towel ta nannad’e jikinta dashi. Gaban dressing mirror ya ajiyeta ya ciro hand drier ya kunna sannan yasoma drying mata gashin bayan ya gama ya mata oiling sannan yayi mata packing gu d’aya harda style na donurt. “Wow! Habeebi you are amazing!” tayi maganan tana duban kanta cikin mirron. “Wai nikam ya akayi ka iya komai neh?” “LOL!” yasoma feeling. “Kin manta inada sister ne?” “Thank you so much for making my hair.” “Always Flower.” Yayi maganar yana mata murmushi miqewa tayi tare da pecking nasa a both kunatunsa, sekuma tip na hancinsa kafin ta kai kan lips nasa ya dakatar da ita. “Uhn-uhn Flower I know where this is going.” Murmushi cike da kunya ta saki “then let it happen.” “A’a Flower kin tuna meh Dr. Yace? Cemana yayi kina buk’atan atleast 3 months na hutu before you can get pregnant again.” “Toh ai hutun d’aukan ciki yake nufi bawai totally mubar yin...” Sekuma tayi shiru “ai ka gane me nake nufi.” light red lips nasa yayi pouting “ban gane ba” yayi maganar da gira d’aya a d’age. Bugi cike da shakwab’a takai masa a hannu “wallahi qarya kake ka gane.” Dariya yake sosai “toh naji na gane but even still Flower muyi hak’uri.” “Toh baby ba semuyi using protection ba.” Kai ya girgiza mata “I don’t trust in that, saboda sometimes suna bursting kuma kinga zaki iya samun ciki if that happens which is very harmful to your condition” ya tab’a tip na hancinta. Baki ta murgud’a masa “ina ni kayi rejecting yau Mr. Fauzi nima sena rama.” Hannayenta ya gwada rik’ewa da wuri ta fisge ita a dole tayi zuciya. Daidai zata juya masa baya kenan ya zagaye hannayensa a waist na tare da pulling nata closer to him. “Haba Mrs. Fauzi matar Anas, the mother to my awesome kids in shaa Allah. Taya zanyi rejecting the perfect woman I’m lucky to call my wife? Kema kinsan hakan k’arya ne, Flower ni kaina ina missing naki like hell I miss us on bed amman kinga lafiyarki ya fiye min komai, koda na shekara da shekaru akace inyi avoiding naki zanyi inhar hakan ne ze sama miki lafiya balle ma na d’an months, bawai nayi rejecting naki bane understand kinji? I’m sorry my sugar lips” Kafad’a ta buga uwar zuciyar har yanzu bata sauk’o ba. “Flower meh kikeso in miki ki hak’ura?” “Muje mu kwanta.” “Zamu kwanta amman ba abinda ze shiga tsakaninmu its a deal.” “O’o toh na fasa hak’uran.” “Sena sauk’a akan knees d’ina zakiyi?” Ganin yasoma sauk’a tayi sauri ta hanasa. “A’a please baby don’t na hak’ura but can I kiss you atleast Mr. Fauzi?” Murmushi yamata “ofcourse Mrs. Fauzi” sannan yayi owning lips nata da kansa yasoma kissing nata.*** **** Tun daga ranan rayuwan masoya biyu ya cigaba da kasancewa kamar yadda ya saba da a baya ko inche fiye dana da ma, ba fad’a kullum cikin farintawa juna rai suke, ga uban lovely suprises da Anas yake cikin bawa Flowersa a kullum. A kullum wutan soyayyan junansu dad’a ruruwa ya ke a birnin zuqatansu. ★★★★ _6 months later..._ _Monday, 6:20AM_ Tsaye Fannah ke a kitchen da shiganta kusan minti uku kenan yanzu amman takasa tsinana komi ciki dan wani irin zazzab’in da takeji wanda ya fara mata tun jiya da daddare amman sam tak’i nuna wa Anas saboda batasan sasa cikin damuwa ‘cause ta lura aduk lokacinda batada lafiya Anas yafita damuwa. Tsugune take gefen sink takasa koda miqewa, tafi minti biyar ahaka sannan da k’yar ta miqe sanadiyar amai da yazo mata, cikin sink d’in ta riga kwararo amai wane zata harar da hanjinta seda tayi emptying cikinta kap sannan ta wanko bakinta, wane k’adangare tabi jikin bango har izuwa d’akinsu. A kasalance ta miqe agefen Anas dake ta bacci hankali a kwance. “Habeebi” ta kira sunansa ko motsawa beyi ba se a karo na uku yayi groaning “uhmmm Flower.” “Habeebi ka tashi kaji? Yau Monday akwai office.” A hankali ya bud’e idanunsa kallo d’aya yama Fannah yagano batada lafiya she is looking so pale. Cike da tashin hankali ya shafa fuskarta “Flower are you okay?” Kai ta girgiza masa “Habeebi I’m sick ko breakfast na kasa had’a maka, I’m sorry.” “Subhanallah, shhhh! Haqurin me kike bani?” body tempreture’nta ya tab’a yaji ya hau sosai yayi zafi. “Omg! Flower kinji tempreture naki kuwa? Ya kikeji?” “Zazzab’i Habeebi sau biyu nake amai yau ko miyau ban iya had’iye.” “Omg! Flower mesa baki fad’amin ba?” I’m sorry kinji?” Kai kawai ta girgiza masa dan batajin ma zata iya magana. “Arghhh!” Ta saki wani irin k’ara hannunta rik’e da gefen cikinta, cike da tashin hankali yakai yana dubanta “Flower wani abu ne?” “Habeebi ciki na tanan, wayyo!” “Sannu Flower ina zuwa” bayi ya fad’a a gurguje yayi wanka sannan ya had’o mata black tea tare da b’allo mata meds. Duk’unk’une cikin bargo ya tarar da ita “Flower tashi ki zauna kisha magani kinji?” Da k’yar ya miqar da ita tare da jinginata jikin gadon, magunan ya miqa mata sam tak’i karb’a. “Flower kiyi hak’uri kisha if not baraki warke ba.” Kai ta kad’a masa nufin barata sha ba. “Why?” Ya tamabayeta. “Habeebi kasan meh?” “A’a meh?” yayi maganar ba alaman kwanciyar hankali tattare dashi. “I think I’m pregnant gani nake kamar ciki ne dani” Bright blue eyes nasa ya zaro waje “Flower you are what?!” Yayi exclaiming cike da k’in yarda dan yadda jin dad’i ya mamaye masa fuska da zuciya. “I’m pregnant again Habeebi kaga ko bareyi insha kowani irin magani ba it may harm our baby.” Tsantsan jin dad’i har a yanzu Anas yakasa believing. Besan a lokacin da ya ajiye tean a gefe ya rungumo Fannah ba. “Flower we are soon going to be Daddy and Mammy again, I love you!” Hugging nasa back tayi dukda ba dad’in jikinta takeji ba. “Yes Habeebi” breaking hug d’in yayi tare da riqe hannayenta biyu cikin nasa “Flower dagaske kike you are pregnant?! Omg! Akwai little Fauzi achan? Ko inche akwai HANAN namu a chan?” murmushi tamasa tana gyad’a kai, hot kisses yahau peppering mata a fuska yana sauqowa kan wuyanta tasa hannu da k’yar ta iya ta shuresa “Habeebi please kadaina, kabari banaso.” Cike da mamaki yake kallonta “bakiya son sugar lips naki yau?” Kai ta gyad’a tana turo baki. D’an murmushi ya saki another symptom yace a ransa “I know this attitude cikin nema dake amman your last pregnancy ai bakiya hanani kissing naki wannan kuma ko kiss d’inma bakiya so?” Nanma kai ta gyad’a. “Humm! Akwai babban aiki Flower ‘cauae I can’t stop kissing you, yanzu kisha black tea d’in seki kwanta zuwa 10 haka se muje asibiti.” Kai kawai ta gyad’a masa shida kansa yabata tean bayan data gama sha ya kwantar da ita. “Habeebi kaifa baraka je office ba?” “Mom Hanan bata da lafiya inje office inyi meh? barinje ba zan sanar da Kacallah.” Kai kawai ta gyad’a masa “thank you.” “Always Baby Machine” yayi pecking nata a kumatu. Hannu tasa ta goge “Habeebi banaso.” D’an murmushi ya saki sannan ya koma d’ayan side d’in ya kwanta tare da janyota zuwa chest nasa ahaka suka koma bacci. 10:30AM Anas ya tashi banda Fannah data kasa bacci tun d’azu se juyi take ajikinsa. Jikinta yayi zafi tamkar wuta shi kansa Anas seda ya razana. “Flower” ya kira sunanta cike da tausayi. “Na’am Habeebi” tayi maganan tana kakkarwa. Kodaya gwada d’gata daga cikinsa sake kankamesa tayi not letting go. “Flower sannu kinji? D’agani mu shiryaki muje asibiti.” “Habeebi mubari anjima ban tsammanin zan iya tashi.” “Sorry kinji? Yi hak’uri” da k’yar ya d’agata ya kaita bayi cikin 30 minutes suka shirya zuwa asibiti achan aka duba Fannah aka tabbatar wa lovely couple cikin sati uku ne d’auke da ita. Murna gun Mr and Mrs Fauzi kam baya misantuwa Anas promised to protect his child with his life wannan karan. **** Tun isowarsu gida Fannah keta tufar da miyau, ga kuma amai a asibiti ma seda tayi dawowansu ma haka, Anas is so worried ko kad’an bara’a had’a laulayin cikinta na farko da wannan ba, bata iya cikakken minti biyu a tsaye se jiri ya kwasheta. Sede bataji k’amshin turare ba in bahaka ba setayi amai na turaren wutan daya mamaye mata gida ma haushinsa takeji. Sallan Azahar ma sauran a zaune ta k’arisa, lunch da Anas yayi musu ma kad’an ta iya tachi shima ta harar. Hankalin Anas yayi matuqar tashi zaune yake akan kujera a gefenta, damuwa ne karara a fuskarsa, ayayinda take kan gado lullub’e da bargo se zufa takeyi. Hannunsa dake akan bayanta ya d’aga dan irin zafin da jikin nata yayi sannan ya share mata zufan. “Sannu Flower, you’ll be fine in shaa Allah I’m here for you.” Moderate cold water ya nemo da towel yana mammatse mata jikin ko ze d’an sauqar mata da body tempreture cikin ikon Allah kuwa zafin jikin nata ya ragu sede bada jimawa ba ya sake rising. Tausayin Fannah duk yabi ya mamaye Anas sam bayason ganinta ba lafiya haka fa suka kwana cikin wannan zazzab’i ba wanda yayi bacci cikinsu se jinyarta Anas yake gabad’aya hankalinsa yabi ya tashi wani irin pegnancy sickness ne haka? _Washegari..._ Rashin lafiyar yau yama fi na jiya ko meh taci seta harar banda black tea tun Anas na iya jurewa har ya kasa Dr. Mansoor ya kira yazo ya sake duba Fannah har ruwa seda aka sa mata, cikin kwana biyu Fannah tazamo abinda tazama ko k’wararren motsi batta iya yi. Maminta Anas yakira ya sanar da ita halin da ake ciki aiko ba tare da b’ata lokaci ba taje tasamu Afrah dake miqe kan gado se hirarta take sha da dearheart nata. “Ke katse wayar” cewar Mami dake tsaye akan Afrah dako noticing shigowar Mami batayi ba. A firgice ta katse wayar, hannunta dafe kan k’irjinta “kai Mami dan Allah yaushe kika shigo? Kinfa bani tsoro.” “Bansani ba kinsa soyayya agaba ina zaki sani dama, mschw! Yarki ba lafiya amman ko a colar rigarki.” “Fannah?!” Tayi maganam ido a waje. “Eh mana yanzu Anas yakirani yake sanar dani. Maza maza tashi muje mu dubata wai har ruwa aka sa mata.” “Oh! Allah sarki Ya Fannah kode wani cikin ne Mami?” “Mukaje ma sani oya tashi kishirya.”**** *_GWS FLOWER, MOM HANAN😔_* *Ina me baku hak’uri and inason ku k’ara hak’uri da irregular posting kwana biyu, somethings came up so se harkoki suka min yawa* *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:59, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 8⃣8⃣ Kuka ne kawai Mami batayi ba kafin securities na wajen suka barsu suka shigo har take cewa aranta barata sake zuwa gidan Fannah ba ko Villa albarka. Bayan Anas ya bud’e musu k’ofan yamusu sannu dazuwa da Mami tayi oberseving fuskarsa kuwa setaga kamar shi d’inma baida lafiya, batasan saboda yadda ya damu da rashin lafiyar Fannah neba harshima yake affecting nasa. “Anas kaima bakada lafiyan ne?” Murmushin dole ya k’irk’iro. “A’a Mami mushiga daga ciki, she is inside.” Bayansa sukabi zuwa d’akin. “Mami” cewar Fannah cikin wani erin murya. “Subhanallahi Habibti” tayi maganan tana tab’a tempreture’nta. “Sannu kinji? Sannu, Anas meke damunta haka?” Shiru yayi yana nazarin taya ze fara sanar da ita face-to-face. Ganin baida na cewa Fannah ta amsa ta “Mami munje asibiti aka tabbatarmana juna biyu ne tattare dani.” “Kai toh Alhamdulilah, Alhamdulilah Anas shine baka sanar dani jika nane yakusa ko ta kusa isowa ba?” K’eyansa yashafa cike da kunya. “Toh Habibti Allah raba lafiya, sannu kinji? Wannan daman ai is normal nan da ‘yan satuka zaki dawo kanki na da se hak’uri.” “Sannu Ya Fannah, Allah raba lafiya” cewar Afrah tana yimata wani shu’umin kallo. Kai kawai Fannah ta kad’a mata. “Kina iya cin abinci?” Kafin ta amsa Anas ya amsa “a’a Mami tun jiya ba abinda tasha banda black tea.” “Toh ya kikeso d’an naki yay k’wari in bakiya chin abinci iyyeh Fannah?! Afrah zaki koma gida yanzun nan ki taho min da gauta dakuma zogale mu had’a mata miya ta samu taci.” Anas da bashi akace zechi ba shine yakai hannu bakinsa ya rufe kan wanda zeyi amai. “Mami is it necessary? Flower zaki iya chin miyan gauta koh? Zaki iya chi?” Kai ta girgiza masa. Kan gadon yanufa ta d’ayan side d’in ya zauna “zakici louisiana ko bufalo wings?” “Habeebi black tea nakeso.” “Toh ai kinji Mami tace baby’nmu will not be healthy in bakiya chin abinci, ko in miki frying sausage?” “Ni black tea nakeso” Kallonsu kawai Mami take “kun gama?” ta tambayesu. Shiru sukayi suna kallon ta. “Nace kun gama? Afrah wuce gida ki d’ibo min gautan.” “A’a Mami please abin beyi zafi haka ba” cewar Anas yana dakatar da Afrah daga tafiyar. “Akwai ragowar glorified rice na jiya zan mata reheating tachi.” “Shi glorified rice d’in kenan? Anas kaga fa duk wannan abubuwa na shirmeh ba taimakanta zasuyi ba kabari taci tuwo d’anku yasamu lafiya maza jeki Afrah.” Anas kan yayi kuka. Nan da nan Afrah taje ta dawo, Mami tashiga had’a miya bayan ta gama ta kawo d’akin da tuwon semovita. Take warin miyan gautan ya mamaye d’akin. “Habibti tashi kichi, kinji? sannu.” Hanci Anas ya toshe dan warin da miyan ke masa he can’t believe Mami zatasa masa Flower cin wannan abu shi dayasan haka ne ze faru da be kira taba in the first place. Da kanta ta zaunar da Fannah ta soma bata, loma biyu Fannah tayi tajawo bowl tayi amai ciki hakan ba shi ya hana Mami sake d’ura mata ba. “Mami please ya isa haka nan karta sake hararwa.” cewar Anas cike da tausayin Fkowersa. “Anas kasan me nakeso dakai?” Kai ya kad’a mata hankalinsa na akan Flowersa ganin yadda batason chin abincin hankalinsa ya sake tashi. “Kaja Afrah ku fice kubani gu in bata abincin nan, nasan tsayunwanka nan ke hanata ci, in baka nan ita da kanta zata zage taci tashi kufita.” “Habeebi please karka tafi kace mata banaso” Fannah tayi maganar kamar wacce zatayi kuka. “Fannnah banason shagwab’a fa tuwon nan da kike gani shi ze baki k’arfi ba wannan ruwan da ake ta d’ura miki wanda banda kumburi ba abinda ze saki ba” tayi maganar tana bin ledan ruwan da aka sawa Fannah da kallo. “Anas jiranka fa nake.” ta miyar da kallonta a garesa. “Da k’yar ya miqe amman yakasa barin d’akin. “Mami please kibita a hankali kinga batada lafiya.” “Naji zan bita a hankali fita ina jiranka.” Badan yansaso ba yafice Afrah tabi bayansa. Haka Mami tasa Fannah agaba ta riga d’ura mata miyan gautan kamar ba gobe tun tana hararwa har tadaina yazauna acikinta. “Good anjima kad’an kuma zakici miyan zogalen shima yana da amfani sosai, sannu koh?” “Mami kasheni kikeson yine? Dan Allah ya isa ni kitafi ma.” “Ai ina nan Fannah kinga yadda kika zube kuwa? Ace mahaifiyarki na raye amman kikayi wannan rama? Wannan abu da keda Anas kuka raina shi zai taimaka miki bawani bufalo wings ne komeh abin ban ma san shiba.” **** Tun kamin Azahar Mami ta tura Afrah gida gudun kar Aiman ta dawo ba kowa gida itako se bayan La’asr Anas yayi dropping nata bayan tabawa Fannah miyan zogalen kuma alhamdulillah bata harar ba, kunne sosai tajawa Anas da yadaina biye wa Fannah yana barinta tana kwana da yunwa, sauran ragowar tuwon kuma ya tabbata yabata zuwa dare in bahaka zata dawo gobe tabata da kanta. Kafin Anas ya dawo gida Fannah tariga tayi bacci, wani sabon ruwa yasa mata kamar yadda Dr. Mansoor ya koya masa sannan ya rage kayan jikinsa ya haye gadon shima tare da aza kanta a k’irjinsa yana me shafa bayanta a hankali anan shima yasamu yayi bacci se Maghrib ya tashi yayi alwala ya tayata tayi itama sannan yajasu Sallah, jikin nata alhamdulillah tunda har tasamu tayi Sallah duka a tsaye. Tana manne a jikinsa jiki ba k’arfi tace, “Habeebi zansha black tea.” Kai ya girgiza mata “Flower kinga Mami tace kar inbarki kina shan tea zallah tace se in kinci tuwon d’azu inbarki kisha tea.” “Habeebi wallahi tuwon ba dad’i please ka had’amin tea.” “Mom Hanan I know” yayi pecking goshinta “kinason Hanan koba haka ba?” Kai ta gyad’a “good then eat well se Hanan namu tafito healthy, kinji Mom Hanan?” Shiru tayi bata ce komai. “Yawwa Mom Hanan tashi inje in d’ebo miki toh.” Koda ya kawo abincin k’inci tayi da k’yar cike da dabara yasata ta soma ci har ya gama bata bata harar ba anan ne ya had’o mata black tea ya bata. Bayan sun idda Isha yasa mata last drip nata suka kwanta. Washegari ma da zazzab’i ta tashi sede ba kaman na jiya ba nayau da d’a sauk’i, kamar yadda Mami ta buk’acesa ya mata reheating tuwon jiyan yau harda ‘yar kukanta dak’yar yasamu taci sam batason ci gashi kuwa shi kad’ai ne in taci bata hararwa bayan shi duk wani abinda takai baki seta fito dashi waje. Da rana Mami ta turo Afrah da miyan ayayo da d’anyen kub’ewa duka a had’e. Fannah kamar ta k’urma ihu shikansa Anas dayake bata amai abincin ke sasa amma haka ze dage yabata. ★★★ Mami bata fasa kawo wa Fannah miyar gargajiya ba, acikin ikon Allah Fannah ta fara samu sauk’i in two weeks time tadawo old self nata sede sometimes da take tashi da morning sickness, jiri dakuma k’warnafi bayan nan bawani ciwo again. Babynsu da suka bata ko shi suna Hanan kuwa nan cikin k’oshin lafiya. Yau ranar ta kasance Sunday Fannah na zaune akan dining table ba abinda babu shi agabanta inde kayan k’walama ne sauran ma ba iya cinsu ta iya ba amman tasa Anas ya siya mata ta tab’a wannan ta tab’a wancan ayayinda Anas ke a parlour se famana latsa wayansa yake da alama abu very important yake dan yadda yayi focussing akai. Chan data gaji da ciye ciyen nata ta tattara ragowar tasa cikin leda sanna ta miqe, sanye take da baggi T shirt da befi tsakiyan cinyarta a tsayi ba da hannunsa d’aya an jefar, gashinta kuwa takamasa gud’aya chan a saman kanta, zare zaren ragowan da basu samu shiga packing d’inba na akan fuskarta kasancewar sakwa-sakwa tayi packing d’in. Parlourn ta iso ta baje kan cinyansa ko uffan bece mata ba se harkar gabansa yake. “Habeebi” ta kira sunansa tana kallonsa. “Uhm Mom Hanan what is it? Har kingama shanye duk tarukuchan dake kan table d’inne?” “A’a.” Ta basa takaicaccen amsa. “Toh me kikeso?” Har a yanzu be d’ago kai ya kalleta ba hakan ya d’an b’ata mata rai. “Habeebi wai me kake haka da ko kallona baraka d’ago wannan blue eyes nakan barakayi ka kalleni ba.” Seda ya sake latsa wayan na kusan seconds talatin sannan ya d’ago blue eyes nasa “yes Baby machine me zan miki?” “Bansani ba seda ka gama replying nata kasan ina a raye ka cigaba da abinda kake” kafin tace zata tashi ya zagaye hannayensa a ‘yar kunkuminta ya dakatar da ita. “Wani irin magana kuma kike Flower? Yanzu har kina tsammanin akwai macen da zata iya snatching maki ni a duniya? (ko Fans albarka😜) i’m not replying any gurl kiduba wayana kigani.” “Eh daka yi deleting chat d’inba ai nasan baka sonmu da Hanan yanzu.” “Flower wai mena miki yaune kam? Naga alaman ba abinda ke miki dad’i kamar kiga kin k’untatamin, niko meh kikamin it will never change the love I have for you” daidai zeyi kissing nata kenan tasa hannu ta riqo lips nasa “kad’au yau ma wannan magic kiss nakan zeyi tasiri akaina neh? Toh bareyi ba sakeni nikam.” Sake matso da ita jikinsa yayi “tell me Mom Hanan why are you mad?” “Aww ma tambayana kake koh? Bayan tun d’azu kake ta danne dannen ka a wayanka baka damu ko *_INA TARE DA KAI_* ko bana *_TARE DA KAI_* ba, your phone is more important than me.” “Inji waye Mom Hanan? Kinason kisan me nakeyi a wayan neh?” “Banaso ai na riga na san-” bata k’are maganan ba yayi shutting nata dawani hot kiss sam tak’i basa had’inkai a farko dan tasan sa sarai he is such a bad kisser nan danan zesa ta mance da dukkannin problems nata ta yafe masa ba tare da tasan tayi hakan ba, sam yak’i sake ta, ya d’au alwashin se ya kashe mata jiki liqis tukuna, yana meh bin duk wani saqo a jikinta da hannayensa yana meh mata sending electric sparks. Ai duk yadda tayi dan k’in basa had’in kai ta kasa daga k’arshe seda tayi giving in wa kiss nasa, ta sa hannayenta duka cikin gashin kansa pulling him closer, se kissing juna suke so deeply, sun d’au tsawon lokaci suna abu d’aya sannan da hanzari suka hau romacing junansu ganin abin bana tsayawa bane na bugo legediz benz d’ina na rufo musu k’ofar parlourn harda cin tuntub’e na. ****_An hour later..._ “Nikam kabar kallo na da wannan mayun blue eyes naka haka bad boy kawai.” Fannah tayi maganar tana mayar da T-shirt nata jiki. Anas kuwa na a kishingid’e jikin 3 seater da nickers zallah a jikinsa, ya yi crossing arms nasa a kan chest da wani killer smile a fuskarsa yana mata wani mayen kallo next abinda yaji shine shirt nasa da Fannah ta wurga masa a fuska, hannu yasa ya cire har a yanzu bebar murmushin ba. “Flower menayi kike cemin bad boy?” “Ai kafi kowa sani” daidai tazo wucewa ta gefensa kenan yajata ta fad’a jikinsa ya saketa sam yak’i. “Bansani ba tell me” yayi maganar numfashinsu na had’ewa dan yadda fuskokinsu ke kusa kusa. “Gashi kuwa I can’t resist you koda nace barin baka had’in kai ba at last senayi because you got it all Abu Hanan.” Pecking nata yayi a kumatu “so do you Mom Hanan.” Kanta tayi adjusting a jikinsa sannan tace, “Habeebi meh kakeyi amman d’azu a wayan?” “Baby Mamah bakiyi trusting d’ina bane?” “Nayi mana Habeebi kawai ina son sani ne.” “Okay kinsan yau Baba yacika 1 year 10 months da rasuwa koh?” “Ya Salam! Habeebi wallahi na mance I’m so sorry kaji?” “Is okay nasan bada gangan kika manta ba, ban tab’a fad’a miki bane saboda aikin lada ba’a son ana yad’awa, so kowani 2-2 months nake sa akai kud’i da kaya gidan marayu in memory of Baba.” “Owww! Kayi tunani me kyau Habeebi, Allah tura masa ladan kabarinsa kaikuma Allah cigaba da bud’i dakuma kare mana kai, Hanan and I love you so much.” Tayi pecking nasa shima a kumatu.**** _3 weeks later..._ Daidai cikin Fannah nada 8weeks (2 months) kenan alhamdulillah jikinta da sauk’i sosai. Yau ranar ta kasance Monday as early as possible k’arfe 4:30AM Anas ya tashi shikad’ansa yahau shirya musu akwatinsu shida Fannah, suprise yakeson mata. Duk wani abinda zasu buk’ata be bari a baya ba seda yagama had’a komai sannan ya d’au ‘yar k’aramar hand luggage ya cika da kayan wasa da teddies na Baby Hanan kafin Asubah yagama had’a komai ya ajiye boxes d’in a parlour yadda Fannah barata gani ba. **** Fitowan Fannah daga bayi kenan tayi alwala, ta d’au hanyan wardrobe nasu dan ciro hijabinta Anas yayi sauri ya dakatar da ita “Mom Hanan wait hijabi kike nema koh?” Kai ta gyad’a masa. “Good gashi.” “Thanks amman banason wannan yanada nauyi nafison d’ayan barin d’auko yana cikin wardrobe d’in ai.” Gabanta yasha sabida kuwa duk hijabanta masu laushi yasa su cikin akwatin bayason ta bud’e wardrobe d’in tayi ruining suprise daya tanadar. “Habeebi wai me haka? Muna chin lokaci fah, kamatsa in d’auko hijabi na muyi Sallah.” “Ga wannan kisa.” Ya miqa mata k’in amsa tayi “banason wannan yanada nauyi.” “Toh nikuma nace kisa wannan.” Haba manah! Habeebi so kake in jik’e kafin mu idar da Sallan ne?” “Flower ai sanyi ake karb’i kisa mana.” Kafad’a ta buga “ni banaji, matsa min.” AC’n d’akin ya k’ure “kinji sanyi ake karb’a kisa.” Seda ta galla masa harara sannan ta amsa tasa bayan da suka idar da Sallan ta nad’e hijabin as always zata miyar cikin wardrobe d’in, takai hannunta kan handle d’in kafin ta bud’e Anas ya dakatar da ita ta hanyan sa hannunsa akai seda ta firgita. K’irji ta dafe “Habeebi kasan ka ban tsoro please kadaina what if wani abu yasamu Hanan fah?” “I’m sorry in shaa Allah ma ba abinda ze sameta kawo in ajiye miki jeki kwanta.” Kallonsa tayi na ‘yan lokuta. “Habeebi wallahi you are hiding something from me, meh abun? Kuma mesa bakason in bud’e wardrobe d’in dakaina?” “Saboda Dr. Yace in hanaki yin any form of labour kuma ai bud’e wardrobe ma aiki ne, prince charming naki ze miki jeki kwanta.” Har a yanzu bata yarda ba. “Sekuma meh? There is still something you are not telling me.” “Oh! Mom Hanan kin cika bincike sekace wani spy” Turata gefe yayi ya sa hijabin sannan yaja hannunta suka koma suka kwanta. Daman tun jiya ya sanar da ita bareje office ba yau dan haka tasamu takwanta peacefully. _8:07AM_ *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:59, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 8⃣9⃣ Daidai tashiwan Anas daga bacci kenan, da k’yar ya iya ya raba jikin Fannah da nasa dan wani sabon salon baccin da ta koya bata bacci se in akansa. Bayan ya tura ta gefe yasake lullub’eta da bargo sannan yayi pecking nata a goshi. Bayi ya nufa yayi wanka agurguje yasa mint blue shirt da farin ¾ wando. Kitchen ya nufa yasoma had’a musu Chocolate-chip cookies for breakfast, in less than an hour yagama komai se coffee daya had’a musu, dining table ya shirya tsab sannan ya koma d’aki dan tayar da ita, zaune ya tarar da ita se murza idanunta take. “Good morning Flower har kin tash-” besamu daman k’arisa maganan ba dan yanayin daya tsince ta ciki kamar kuka take, daya gama k’arisowa kusa da ita kuwa seya tabbatar da hakan zama yayi a gefenta. Cike da tashin hankali yake maganar. “Omg! Flower why are you crying?” Kasa amsa shi tayi kawai tayi hugging nasa a yayinda kukanta ya tsananta. Bayanta yake bubbugawa a hankali, “shhh! Kibar kuka kinji I’m here stop crying Flower” seda ya tabbata tayi shiru ya d’agota. “Meya faru?” “Habeebi promise me baraka tab’a barina ba, promise me please.” Ta sake matsesa ajikinta tana meh cigaba da kuka. “Shhh! I will never leave you Fannah, never ki kwantar da hankalinki *_INA TARE DA KE_* forever.” Hannu yasa ya share mata hawayen ”meya kawo wannan zance? Kinyi mafarki ne?” Kai ta gyad’a masa. “You want to talk about it?” Nan kuma ta kad’a mai kai “I’m afraid Habeebi.” “Toh shikenan is okay, tashi kiyi wanka yanzu.” Ba musu ta miqe ta amshi towel dayake miqa mata bayan ta cire kayan jikinta ta d’aura towel d’in “Habeebi ka rakani bathroom d’in wallahi tsoro nake wai Ya Farouq na ciki.” “Mafarkin Farouq kikayi dama?” Cike da tsoro ta gyad’a kai. “Karki damu Farouq is gone foever.” “Nasani Habeebi still ina tsoro ka rakani please” hannunta ya riqe yakaita har bathroom d’in tabarsa yafito tak’i labule taja ta tare kanta shiko yana zaune akan hand basin bayan data gama suka fito tare man shafawanta ta nema kap kan mirron babu. “Habeebi kaga lotion d’ina?” Se ayanzu ya tuna ya had’a cikin akwati d’azu. “Bangani ba Flower, babu akan mirron?” yayi qarya. “Babu” tayi maganar tana nufan wardrobe dan ciro sabo. “Wait wait!” yayi sauri ya dakatar da ita, “babu achan ga vaseline chan ki shafa.” “Habeebi wai me kake b’oyewa cikin wardrobe d’innan ne?” “Kan Farouq ne aciki kika kuskura kik-” be samu daman k’arisa maganan ba sanadiyar tsallen da Fannah ta daka se a jikinsa ta tsaya chak! hannu yasa ya tare ta kafin ta fad’i. “Na tuba wallahi barin bud’e ba, dan Allah kabari ina vaseline d’in zan shafa.” Dariya sosai ya tsaya yi “toh muje mu shafa miki amman sauk’a tukuna.” ya gwada cire hannyenta dake rataye a wuyansa, kafad’a ta buga nufin barata sauk’a ba tare da sake kankamesa, haka tana zaune kan cinyarsa ta shafa manta. Kayan ta daya cire mata wani baqin abaya ya miqa mata, “gashi sa.” “Habeebi abaya nefah.” “Ina sane ai” ya gyad’a mata kai. “Toh ina zamuje da zan sa abaya?” “Ikon Allah! Mom Hanan ko d’an bincike seya baki hanya wani irin bincike ne haka?! Allah kika sake questioning d’ina zan bud’e wardrobe d’in Farouq yafito.” “Nabari nabari please kabar fad’in sunansa Hanan zatayi kuka.” “Toh Mom Hanan na dena” yayi managar hannunsa na akan cikinta. “Flower yaushe Hanan zata soma motsi I want to feel her.” “Dr tace se pregnancy’n yakai zuwa 16 weeks and Hanan is just 8 weeks yanzu kaga da saura.” “Ohh kice min se cikin ki yayi k’aaaatoo Hanan zata fara motsi.” Hannunsa ta d’aga daga kan cikin nata “nifa na fad’a maka bawai wasan nan na sani dariya bane banaso.” “Toh I’m sorry yi sauri kisa kayanki.” “In nasa ina zam-” bata k’arisa maganan ba tayi tsit dan ta tuna da abinda Anas yace mata akan ta sake masa tambaya ze ciro kan Ya Farouq cikin wardrobe. Kamar baby ya riqota a hannu zuwa dining table yasan ta da kewaye kewaye kar idanunta sukai kan akwatinan nasu. “Habeebi harda breakfast kamana yau wow!” Yana bud’e flask d’in k’amshin abincin ya mamaye wajen gabad’aya se shaqa Fannah ke tana d’igan miyau. “Baby hurry up and serve me yunwa nakeji.” “Kwad’ayi kike ji de.” K’aramar tsuka taja ta bugesa gefe ta amshi flask d’in taja gabanta ta soma chi. Tsayuwa yayi yana kallon ta cike da mamaki ganin takusa cinyewa ba shi yayi magana “Flower nifa ban chiba karki cinye duka.” “Ayyah Habeebi, Hanan kuma fah? Kayi hak’uri kabarmu mu cinye mana.” “Bawani Hanan d’innan glutton (meh shegen cin abinci) kawai.” “Kafad’i koma meh mu cinye?” Kai ya gyad’a mata yana murmushi yadda takecin abinci na bala’in kashesa. Bayan da ta gama yaje yayi frying sausages ya karya dashi shima. Bayan da suka gama ya tattara dining table d’in “Flower jekisa mayafin abayan naki we are going somewhere.” “Ina kenan Habeebi?” “Aww! inje inciro kan Farouq ko?” “A’a please nayi shiru.” “Better jeki shirya ina jiranki and karki bud’e wardrobe d’in ni na fad’a miki.” “Toh Habeebi kazo muje tare wallahi tsoro nakeji” seda yayi ta mata tsiya sannan ya rakata yana ganinta tana shiryawa har tagama tayi arabian rolling mekyau me amsarta sannan ta feffesehe da turare d’ayan da kad’ai tagani kan mirron ta tambayi Anas ina sauran turarukanta kuma tana tsoron kar yaciro kan Farouq daga cikin wardrobe. “Kingama?” Ya k’are maganar hannunsa k’ark’ashin hab’anta yana kallon fuskarta datasha light makeup. “Eh nagama semeh kuma yanzu?” “Se...” Yakai bakinsa kan nata “Habeeb-” be sake mata baki ba seda ya tand’e maroon strawberry flavor jan bakin data shafa tas. “Haba! Habeebi” tayi maganar lokacin da ta juyo tana kallon bakin nata a mirror. “Mena sharemin jan bakin yanzu?” Tayi pouting lips nata. “Saboda yamiki kyau sosai and banason in mun fita mutane suna kalla min ke, because you are mine Flower, as from today banason ki sake yin makeup in zamu fita okay?” “Nikam wannan Habeebin” tayi maganar chan k’asa k’asa tana zumbure zumbure. “Yes Flower kajol da nude lipstick kawai na yarda kina sawa kinji?” Shiruu “nace kinji?” “Naji-” katsesa yayi “good, agida kawai na yarda kina kwalya.” “Habeebi gaskia akwai ka da son kai amma kaika iya d’aukan wanka kamar me zuwa gidan biki idan zaka fita.” “Toh mijinki neni ai” be jira ta sake magana ba yajata waje zuwa mota sannan ya dawo ya kai boxes nasu mota dake se game nata take ta bugawa ko kad’an bata ga me yake ba seda ya shigo mota ya tambayeta “Mom Hanan are you ready?” “Do I have a choice bayan baka sanar dani ina zaka kaini ba.” “Karki damu you’ll find out soon.” Seda ta bari sukayi nisa da tafiya ta yadda barasu iya komawa gida ba, balle yace ze ciro kan Farouq tasoma jero masa tambayoyi wanda duk ciki ba wanda ya bata straight answer. Wani tambayan ma seda ta ga sun dosa hanyan airport “Habeebi wai me zamuyi anan?† “Flower inda zaki d’an k’ara hak’uri everything will turn out cool.” Badan tanaso ba tayi shiru waje yanema yayi parking sannan ya fito da ita a yayinda wani security ya cicciro musu luggages nasu “Habeebi wannan fa akwatina ne a hannun mutumin nan” tayi maganar tana bin mutimin da kallo. “Yes ina sane Flower” ya jawota jikinsa. “Toh a ina ya samu?” “Acikin booth kayakin mune aciki.” Cike da mamaki da rashin yarda tsantsan mamaki ta d’ago kai tana kallonsa. “Kayan mu aciki? Kana nufin tafiya zamuyi?” Gira ya d’aga mata. “What?! Habeebi-” yatsansa ya aza a lips nata “shhhh! Nasan me zakice ban fad’a miki ba you are not ready barakije ba but please don’t say so kinji? Don’t ruin this I’ve worked hard for it.” Hugging nashi tayi abinda beyi tsammani ba a tunaninsa she will freak out tace masa barata jeba. Cikin sauti cike da jin dad’i tayi maganar, “Taya zance barinje ba Habeebi bayan nasan you worked hard for it I just hope we will enjoy inda zaka kaimu. Me, you and our Hanan Habeebi.” Dad’in kalamunta yaji sosai yayi hugging nata back “we will in shaa Allah Flower, I love you dearly.” Bayan tayi breaking hug d’in ta ciro wayarta daga jakarta “me zakiyi Mom Hanan?” “Zan kira Mami in sanar da ita.” Wayar ya amsa “don’t worry na riga na sanar da ita lets just go, hope you are ready to go fly to Abuja?” “Abuja? Okay I am ready.” Wajen private jet nasa wanda be tab’a tafiya dashi ba yau ne karo na farko suka nufa se admiring jirgin Fannah ke bata tab’a ganin kalan jirgin ba se a TV. “Habeebi mu kad’ai zamuyi tafiyan ne?” “Yes Flower this is my private jet ba public jirgi bane.” “Ohhh wow! Its amazing baka tab’a fad’a min ba.” “Sorry nima ban tab’a using nashi ba seyau tun kafin muyi aure na saya I mean tun lokacin dana fara sonki Flower I was hoping Allah ze kawo min ranan da zan shiga ciki dake that is when we’ve accept each others love just as we did a very long time ago now, I love you Flower” Kyakkyawar fuskarsa ta shafa “I love you too Abu Hanan.” Hannunta ya riqe suka shiga ciki bayan angama komai da komai sauran tashiwar jirgi Fannah tasa suka karanto add’o’in kariya. Tun anan Anas yagano ta soma jin tsoro dan kuwa this is her first time shiga jirgi. Seatbelts Anas yamusu tighting aiko ta riqo hannunsa gagam “Habeebi na fasa tafiyan ina jin tsoro please su tsaya.” Dariya yakeson yi amman ya b’ata rai. “Flower just keep calm muna tashi everything will be normal.” “No Habeebi ni kawai kace musu su tsaya” a hankali jirgin ya fara tafiya bata wani ji tsoro ba seda jirgin ya fara tashi anan ta fara kuka harda hawaye hannunta Anas ya matse cikin nasa yana fad’a mata dad’ad’d’un kalamu ahaka har suka tashi da suka fara flying kuwa seta bar jin tsoron. A hankali ta bud’e idonta d’aya sannan d’ayan. “Kin dena jin tsoron?” Kai ta gyad’a a hankali “are we flying already?” “Yes Flower we are kiduba window kiga.” “A’a tsoro nakeji.” “Ki leqa ba abinda ze sameki am here.” Cike da tsoro ta leqa kad’an da wuri ta dawo da kanta ciki “calm down Mom Hanan ki kwanatar da hanakalinki ko kinason Hanan ma taji tsoro ne?” Kai ta kad’a masa “good” yace tare da pecking nata, headphone ya ciro yasamata akai tare da kunna mata qira’a. Cikin ‘yan mintuna suka iso Abuja nan ma da suka zo landing kad’an ya rage Fannah batayi kuka ba. Transcorp Hilton Hotel Abuja suka sauk’a zuwa Azahar bayan sunchi abinci sun sake wanka suka wuce embassy’n USA kasancewar a New York Anas yakeson suyi rainon Baby Hanan. Dad’i sosai Fannah taji daya sanar da ita plans nasa, sun gaji iya gajiya wai haka ma dan da sanin ido kenan aka samu aka gama musu abubuwan on time zuwa jibi everything will be ready seya rage sauran tafiya. Koda suka dawo gida Fannah takasa fitowa daga mota dan gajiya Anas ne ya cirota da kansa yakaita har zuwa d’akinsu. Akan gado ya direta kafin ya juya ta riqo kolan rigarsa tajasa jikinta kafin yayi wani k’wararren motsi ta kifa bayansa da gadon ita kuma ta haye kansa. “Habeebi bacci nakeji.” “Flower bamuyi Sallan isha bafa.” “I know Habeebi mubari zuwa 10-11 haka se muyi please.” Shiru yayi tare da aza hannunsa kan bayanta yana shafawa a hankali. In the next 5 minites Fannah tayi bacci. “Flower!” ya kira ta shiru ba amsa. “Flower har kinyi bacci?” “Uhmm” tayi groaning cikin baccin. D’an murmushi ya saki tare da pecking kanta. A haka shima ya samu yayi bacci se 11:27PM Anas ya tashi anan sukayi Sallah suka chi abinci sannan suka watsa ruwa suka sake komawa bacci. Kwanan su biyu a Abuja Anas ya sama masu visa. Washegari around 8:00AM suka d’au flight zuwa New York kamar sabon shiga haka tata jin tsoro ma yau. _10 hours later... Exactly 6:00PM a Nigeria 1:00PM a kuma New York_ Su Anas suka shigo NY gajiya kam ansha sosai, musamman Fannah kusan duk a kwance kan gadon dake jet d’in ta yini amman hakan be hana k’afafunta kumbura dam ba. A MANDERIAN ORIENTAL HOTEL NY suka sauk’a. Fannah de takasa b’oye k’auyancinta inwhich Anas found so adorable and cute komai tagani seta tambaya. Warming jikinsu sukayi cikin had’ad’d’en jacuzzin dake bathroom d’in sannan suka yi ordering abinci sukaci. Baccin sauk’e gajiya suka yini sunayi ranan da daddare bayan sun idar da Sallan isha sunci dinner Anas yahau massaging wa Fannah k’afafunta da suka kumbura bayan daya gama mata kuma suka kwanta. Washegari basu fita ko inaba a d’akinsu suka wuni ba abinda suka tsinana wa kansu banda romancing juna da suka yini sunayi se the next day suka fita ganin gari leisure points da dama erinsu 911 Memorial Guided Tour with Museum, Disney on Broadway Exclusive, Magic Walking Tour, NBC studio, central park, Brooklyn bridge, 9/11 Memorial and Museum, da sauran su suka jejje se killing selfies suke Fannah nawa Afrah da kishi kamar ya kasheta sending. They had alot of fun se Maghrib suka dawo masauk’insu all tired. Sallah kawai sukayi suka miqe kan gado se bacci. Haka fa rayuwa ta cigaba da kasancewa Mr. And Mrs. Fauzi cikin so da k’aunan juna, zamansu a New York ba shiyasa Anas hana Fannah sa hijabi ba dukda kuwa in aka gansu se an tsaya ana kallonta amman kamar yaddda bata damu ba haka shima Anas d’in, sosai yake kishin Flowersa. Baby Hanan nasu kuwa se girma take a yanzu haka cikin Fannah nada 5 months da anganta anga me ciki dan ko har ya b’ullo kai tun anan Anas ya fara neman tsokananta dan haka tama bar zama da vest inya nan se baggi kayakin da zasu b’oye mata‘yar cikin nata, ga yadda taciko dam iya cikowa Anas baya iya hak’ura da ita yanzu aduk lokacin da ya kalleta se sha’awan ta ya taso masa kullum suna cikin yin abu d’aya. **** Yau ranar ta kasance Tuesday ayau ne Mr. and Mrs Fauzi zasuje duban gender’n Baby’nsu tunda cikin yayi k’wari, dukansu bugawa zuqatansu ke barin ma Anas dakeson ‘ya mace kamar hauka. **** Murna gun Anas da Fannah baya misantuwa da aka tabbatar musu mace ce baby’nsu. Sabon siyayya Anas yace zasu soma yiwa Baby Hanan yanzu da aka tabbata Hanan d’ince a hanya, inbawani ikon Allah ba. Ta ward d’in karb’an haihuwa suka fito aiko Fannah na ganin yadda mata masu ciki ke nak’uda yadda suke shan azaba ta rushe wa Anas da kuka. Kuka na sosai seda suka nemi waje suka zauna hankalinsa duk yabi ya tashi ya rasa meya sata kuka haka, just a while ago she was happy jin sex na baby’nta yanzu kuma tana kuka to meh dalili? Ko ta dena san ‘ya mace sena miji ne? “Flower is okay kinji stop crying please ya isa” ya cusa ta ajikinsa yana bubbuga bayanta har izuwa lokacin da tayi shiru. *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:59, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 9⃣0⃣ “Flower mesa kike kuka? Do you want to talk about it?” A nitse ta d’ago kanta daga k’irjinsa ta share hawayenta sannan ta masa nuni da ward d’in. Cike da rashin fahimta yace, “what about it Flower?” “Habeebi baka ga yadda matan suke kuka bane? Yadda haihuwan ke basu wahala Habeebi I’m afraid” tasake rushewa da kuka. Kallonta ya tsaya yi Fannah barata ishesa da kallo ba. Sake kwanto da ita yayi a jikinsa yana bubbuga bayanta “is okay kinji bar kukan ya isa, you will have a safe and easy delivery in shaa Allah zamu cigaba da miki addu’a bar kukan haka ya isa.” “Habeebi ina tsoro kasan wasu matan daga labour room se lahira suke wucewa Habeebi banason in mutu ban rik’e Hanan ba.” “Flower kibar magana haka wayace zaki mutu baraki riqe Hanan ba? In shaa Allah zaki shiga labour room kuma kifito fine and good banason irin maganan nan kinji? Stop crying ya isa.” D’agota yayi sannan ya share mata hawaye “lets go and eat.” Ba musu ta miqe tana manne a jikinsa har suka isa gun motansu. Yana cikin driving ya juyo ya kalleta tayi lamo jikin kujeran tana kallon window. “Flower kinsan you are funny koh.” Ba tare da ra juyo ba ta amsa shi, “menayi kuma yanzu?” “Kukan da kikayi mana, gaskiya banason Hanan ta d’auko kukanki abu kad’an kuka.” “Sekayi ai kai dama in baka nemi tsokana naba bakajin dad’i.” “Oh common Mom Hanan chill please wasa nake miki.” daga nan bata sake che masa k’ala ba. A Restaurant Manhattan Anas yayi parking bayan ya fito da ita daga motan sukayi ciki, table dake kusa da bakin k’ofar ya zaunar da ita a yayinda ya yi ciki dan yimusu order kasancewar traditional restaurant ne. Fannah na zaune ita kad’ai kan kujerar tayi jugum har a yanzu hankalinta be kwanta ba regarding mata masu nak’uda data gani d’azu daga bisani ta d’ago kai tana kallon k’ofar seji take kamar ana binta da kallo data dudduba kuwa se bataga kowa ba. Kamar daga sama taji hannu dafe kan kafad’ar ta a razane ta d’ago kai acewarta ma kidnapping nata za’ayi harta bud’e baki zata sa ihu setaga mace ce ‘yar uwarta anan ne hankalinta yad’an kwanta. Bata tab’a sa matan a ido ba amman kuma she is sure ba a yau ta fara ganinta ba zuciyarta se rad’a mata take she’ve met this woman before amman ta rasa a ina. “Sannu Sister yi hak’uri in na razanar dake please.” matar tayi magana cikin muryarta wanda sosai yayi kama da wata wanda Fannah tasani amman ta rasa gane a ina, no matter how tayi ta tuna a’ina tasan muryar ta kasa. “A’ah ba komai Aunty” cewar Fannah har a yanzu se kallon wannan babbar mace me k’imanin shekaru 45 take tana me tunanin a’ina ta tab’a ganinta. “Toh nagode nace dan Allah wancan da kuka shigo dashi just a while ago mijnki ne?” Shiru Fannah tayi tana nazarin ko ta bata amsa kokuwa kar ta bata saboda question d’in is too private. Shirunta ya sake bawa matar damar magana. “I’m sorry please karkiji tsoro ba abinda zan miki suna na AYSHA kuma ‘yar Nigeria ce nima kamar ku kawai I want to know ne please ki fad’amin.” “Eh mijina ne.” tayi maganan idanunta cikin na Aysha, hawaye ne suka soma gangarowa kan kumatun Aysha wanda yamugun bawa Fannah mamaki toh kode son Anas nata wannan Aysha ke da har zatayi kuka da ga jin ance yanada aure. “Aunty Aysha mesa kike kuka?” “Babu, babu ba komai sunan mijin naki A... A... Anas koh?” cike da mamaki Fannah ke kallonta har taya tasan sunan Anas? Ta bud’e baki zatayi magana kenan Anas yakira ta from far behind. “Flower!” Da sauri ta juya izuwa direction nasa, drinks biyu ne riqe a hannunsa “wannan ko wannan kikeso.” Murmushi ta saki sannan tayi nuni dana hannun daman nasa, ido ya kashe mata sannan ya koma anan ta juyo dan cigaba da magana da Aysha sede ta duba gabas da yamma kudu da arewa bataga Aysha ba. A nitse ta miqe ta fito waje tana kewaye kewaye ko zata ganta amman ko alamarta babu, badan tanaso ba ta dawo ciki ta zauna shima Anas bada dad’ewa ba yadawo da plates nasu a hannunsa nata ya ajiye mata a gabanta. “Thank you Habeebi amman basu da waiters ne sekai zaka kawo mana da kanka?” “Ninaso Flower, kinsan white people d’innan da shegen son mata banason su kalla min ke.” Dariya sosai take “over possessive ba” tace cikin dariya. “Na yarda whatever lets eat.” Cike da jin dad’i suka soma chin abincin daga bisani Fannah tace, “yauwa Habeebi bakasan meba.” “Meneh?” Ya tambayeta tare da kai spoon baki yanacin abincin. “Shiganka ciki wata mata ‘yar babba haka tazo ta sameni take tambayana wai ko kai miji na ne dana tabbatar mata mijina ne kai sekuma tasoma min kuka wai sunan ta Aysha kuma abinda yafi ban mamaki ma yadda tasan sunanka, nayi nayi intuna a ina na tab’a ganin ta amman na kasa ‘cause her face seems familiar.” Spoon daya kai bakinsa ya maido shi plate d’in tare da d’ago blue eyes nasa yana kallon Fannah. Anan data kuma k’are masa kallo itama se ta tuna a ina tasan kamannin fuskan Aysha, anan tagane a’ina ta tab’a ganin fuskar Aysha ashe cikin family photon su Anas ne wanda ya goge fuskarta, anan ta gane Anas nata ke kama da Aysha, muryar Amal kuwa sak na Aysha ce. Aysha itace Ummimin su Anas. Ummimi na raye bata mutu ba. “Kikace meh?” Cewar Anas alokaci d’aya yaji lisafin k’wak’walwarsa na gushewa jin an ambaci Aysha sunan mahaifiyarsa da ya tsaneta fiye da komai a duniya. “Habeebi Ummimi nagani, wallahi ita nagani just a while ago.” “Whaattt?!” Ya tambayeta cike da k’in yarda. “Habeebi itace wallahi itace, Ummimi ce tana raye tashi mu neme ta I know she is somewhere close to us” kafin ta miqe Anas ya zaunar da ita har a yanzu besan meyake ciki ba tunaninsa duk ya jagule kayinsa na juyawa. K’arfin hali yayi yace, “ba ita bace Flower, Ummimi ta mutu inma bata mutu ba tana chan bangon duniya da mijinta da yaranta saboda haka ba ita kika gani ba lets eat and leave this place.” “Hab-” katse ta yayi a tsawace “I said enough ba ita bace!” Ta mugun firgita barata iya tuna when last Anas ya mata tsawa haka ba ‘yar k’ollan dake ciko mata a ido tayi sauri ta shanyesu bata sake ce masa komai ba. Sunfi minti biyu zaune ahaka ba tare da sunce da juna ko uffan ba, abincin gabansu ma duk sun kasa chi as Fannah ta zura wa Anas daya zurfafa cikin tunani ido. _What if abinda Fannah ke fad’i gaskia ne dan kuwa be tab’a fad’a mata asalin sunan Ummimi ba how comes zata sani inhar bawai taga Ummimin bane dagaske. Amman kuma is it possible? Meze kawo Ummimi New York? Dakansa ya amsa wannan tambaya._ _Ai koda tazo tafiya ce mana tayi wanda ze aureta yace ze kaita k’asar waje meaning k’asar waje nan New York ya kawota kenan?_ Kai ya girgiza a sauri “No it can’t be!” yayi maganar a fili. Hankalin Fannah yayi matuqar tashi ganin hankalin Habeebinta ba’a kwance ba. “Habeebi is okay kaji? Ya isa haka Abu Hanan.” tasa hanky ta share masa zafaffun gumin dake k’eto masa. “Lets go” yace da ita tare da miqewa ya riqo hannunta suka fito suka kama hanyan lot kamar ance Fannah juya ta juya idanunta basu sauk’a ako ina ba sekan Ummimi dake tsaye daga bakin k’ofan Restor d’in, sanye take da hijabi bak’i iyaka guiwa fuskarta duk alamun hawaye, kallo d’aya za’a mata agano tsantsan rashin kwanciyan hankali da wahala tattare da ita amman duk da hakan kyawun halittan fuskarta wanda su Anas suka d’auko be gushe ba. “Habeebi” Fannah takira sunansa tare da dakatar da tafiyarta badan yanaso ba yatsaya shima batare da ya raba hannayensu ba. “What is it Flower? Lets go!” Yayi maganar cikin wani erin murya. “Habeebi ka juya ka ganta gata chan” a hankali yake karkato da kansa har ya juya gabad’aya sannan ya d’ogo blue eyes nasa ya miqar basu sauqa ko ina ba se akan Ummimi. Kallonta yake cike da rashin yarda, sam yakasa yarda Ummimi ce yau a gabansa shekaru nawa rabuwansa da yasata a ido? 15 good years, memories na incident daya faru lokacin tafiyar Ummimi ne suka soma masa yawo a k’wak’walwa. “Anas” yaji muryar Ummimi dake nan kamar na Amal na tsamo sa daga duniyar tunanin daya wula, a gabanshi yaga Ummimi tsaye idanunta cike dam da hawaye tana kallon cikin idanunsa. “Anas... My.. My... My son... Anas my son” tasa hannu akan kumatunsa tana shafawa a hankali ayayinda k’arfin kukanta ya dad’u, shi kansa Anas idanuwansa sun kad’a sunyi jazir, he don’t even know what he is feeling fatansa kad’ai Allah sa dukkannin wannan mafarki ne. “Anas my son kamin magana dan Allah.” Hannunta ya sauk’e daga fuskarsa cike da k’in yardan itance a gabansa. “Ummimi?” Ya kira sunanta. “Kece?” “Nice Anas, Ummimi ce mahaifiyarka, Ummimi ce your own very real mother, Anas nice.” Duk yadda yayi dan shanye kukan yakasa besan a lokacinda yasoma zubar da hawaye ba, Fannah dake tsaye a gefensu tayi shiru ta k’ure musu ido tana kallon yadda suke zubar da hawaye. “Anas kayi min magana please” yunk’urin hugging nasa tayi wanda sakamakon haka yaja baya da wuri. Hannun Fannah ya rik’o “lets go Flower” nan ya juya. “Anas!... Anas! dan Allah ka tsaya.” Cewar Ummimi cikin sautin kuka. “Habeebi please ka tsaya ka saurareta kaji please” Fannah tayi maganar tana k’ok’arin tsayar dashi amman sam yak’i saurarenta. Murfin motan ya bud’e mata “get in!” “No Habeebi I’m not getting in, taya zaka bar mahaifiyarka haka?” “Fannah kinga banason abinda ze had’ani dake just get in” zata sake magana ya daka mata tsawa “I said get in!” Shi da kansa yasata cikin motar sannan ya zagaya ya shiga shima ya kunna motar. Ta window Fannah ke kallon Ummimi dake kuka sosai tana bin motar nasu da kallo amman Anas kota kanta beyi ba. **** _Some hours later..._ Zaune Anas ke akan wresting chair yayi shiru, tun dawowansu bema Fannah magana ba itama haka bata huce da masifan daya mata ba d’azu ba, zaune take kan gado tana kallon sa a nitse ta miqe taje ta samesa tana tsaye akansa amman ko kewayowa ya kalleta beyi ba. “Habeebi” ta kira sunansa tare da zama kan cinyansa. “Yes Flower” yayi maganar not paying attention to her, hannunsa ta d’aga ta had’a da nata. “Habeebi I’m sorry for crossing you earlier.” “Is okay Flower ni yakamata in baki hak’uri for shouting at you I’m sorry kinji?” “Ba komai ya wuce muje mu huta.” Kai ya kad’a mata “banajin bacci just go, nap well Baby Hanan” yayi maganar hannunsa kan cikin Fannah. “Mesa baraka kwanta ba Habeebi ba haka na sanka ba tunanin Ummimi kake?” “I don’t want to talk about her Flower jeki huta.” “Habeebi yakamata ka cire son zuciya kayi facing reality, duk abinda Ummimi ta maka kamata yayi kayi hak’uri ka yafe mata, uwa uwa ce yanzu zakaso ace Hanan ta min kalan abinda ka ma Ummimi?” “For God’s sake Flower kidena kwatanta Hanan da Ummimi, Allah raba Hanan da halin Ummimi banason maganan ta karki sake d’auko min maganar ta.” Zata sake magana ya katse ta “am I clear?” Badan tanaso ba ta gyad’a masa kai ta sauk’a kan cinyansa ta koma gado ta miqe. Batasan a lokacin da bacci yayi awon gaba da ita ba. A hankali ya miqe ya nufa wardrobe tare da ciro wallet nasa family picture’nsu ya bud’e yana kallon fuskar Ummimi. “Why do you have to show up Ummimi? Why? Bayan duk mun mance dake munyi moving on mesa zaki dawo ki sake hargitsa mana rayuwa as you did before, why? Mesa bakida tausayi ne?” Ganin bayida amsoshi ga wannan tambayoyi ya haye gadon ya kwanta a gefen Fannah tare da kwantar da ita jikinsa hannunsa na akan cikinta. “Hanan in shaa Allah baraki d’au halin Ummimi ba, baraki ma yaranki abinda Ummimi tama Daddy’nki ba.” Daidai nan Hanan dake ciki tayi kicking take Fannah ta tashi “Habeebi Hanan ta motsa yanzu” murmushi ya k’irk’iro mata “yes Flower nima naji” hannunsu duka suka kai kan cikin nan Hanan tasake motsawa. Dad’i kamar ya cinyesu both suna feeling baby Hanan insu. **** _Washegari 1:30PM_ Anas na tsaye a gaban mirror a bathroom fuskansa shaving cream ne da alama shaving zeyi danko riqe yake da shaving stick a hannu amman sam ya kasa yi, gabad’aya hankalinsa bayya a jikinsa ko bacci yakasa jiya se tunanin Ummimi yake, duk yadda yasan ze iyabi dan hana tunaninta yayi amman ya kasa the more yana hana kansa the more yake tunanin nata, Fannah ma takasa bacci ta zauna awake with him ko kad’an bayason maganan Ummimi koda Fannah ta taso da maganar masifa yake mata sosai wanda shima ba a son ransa yakeyi ba, he just can’t take it. Ya zurfafa cikin tunaninsa next abinda yaji shine hannun Fannah akan nasa tana amsar shaving stick d’in kwata kwata besan lokacin da ta shigo ba. Sanye take dawani silky dogon riga me spaghetti hands. “Habeebi take it easy please banason ina ganinka cikin damuwa.” Juyo da fuskarsa tayi ta soma yimasa shaving d’in lightly kamar yadda take ganin yanayi. Bece mata komai ba har seda ta gama masa ta wanke mai fuskar tare da share ruwan da towel. Kallon kansa yayi a mirron, sosai shaving d’in yamasa kyau saboda bata kwashe gashin duka ba, tabar sajen da kuma beard nasa wanda suka had’e kad’an very light irin na larabawan nan sosai yayi kyau. “Flower kin ma fini iya shaving d’in ban tab’a leveling haka ba” yayi maganar yana shafa kan gashin fuskar nasan. “Thank you sweetheart.” “No big deal Habeebi” Hannayenta ya had’a gu d’aya tare da pecking nasu, “Flower ko baki fad’a ba nasani you are mad at me saboda abubuwan dana riga miki jiya, I’m sorry kinji? I’m sorry for shouting at you and Hanan” “Na sani Abu Hanan you don’t have to be sorry komi ya wuce muje muci abinci amman yau ba anan nakeson chin abinci ba.” “Fad’i duk inda ke da Hanan kukeso muje muchi.” “A Restaurant Manhattan mukeso” (inda sukaga Ummimi jiya) kai ya girgiza mata “no Flower baramu je chan ba choose any other place amman banda chan.” “Ayya Habeebi chan nakeso.” “Flower NO! And that stays that bara muje chan ba.” Ba tare da tace komai ba ta k’wace hannayenta daga nasa ta fice zuwa d’akinsu tare da kwanciya kan gado tana jin footsteps nasa ta soma rera kukan qarya. “Flower yanzu kuka kike saboda nace bara muje chan ba?” Yayi maganar yana k’ok’arin d’agota. Shuresa ta shiga yi “ka sakeni nikam bana so stop touching me.” “Haba Mom Hanan I’m sorry kinji?” “Banji ba ni ka sakeni.” Kunnuwansa ya riqe both “Flower I’m sorry kiyi hak’uri.” Da hanzari ta suk’e hannayen nasa “ni bance kabani hak’uri ka ka kaini Restaurant Manhattan kokuma karka sake min ko Hanan magana.” “Flower kiyi hak’uri mana ki zab’i wani restor daban.” Banza dashi tayi tare da juya masa baya. “Mom Hanan magana fa nake miki...” Nanma shiru “Mom Hanan” still shiru “toh naji tashi muje Restaurant Manhattan d’in” a ransa yana me addu’an Allah yasa kada su had’u da Ummimi. Cike da ji dad’i ta miqe tare da brushing masa ligjt kiss a lips “thats my Abu Hanan! Lets go” kallonta kawai yake cike da adoration. *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [12:59, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 9⃣1⃣ Cike da so da qaunan juna suka shirya suka fita chin lunch a restaurant Manhattan kamar yadda Fannah ta buqata, bayan Anas ya kawo musu order’nsu suka soma ci cike da jin dad’i, sosai Fannah ta zage ta gabza abincin se kewaye kewaye take ko zata ga Ummimi daga bisani k’ofar restaurant d’in ya bud’u atare Fannah da Anas suka miyar da kallonsu wajen Ummimi sukaga tsaye wajen tana rik’e da leda da alama shopping tayi sanye take da rigan cleaners, mamaki ne fal kwance kan fuskokinsu musamman ma Anas _bade Ummimi aiki take anan as a cleaner ba?_ ya tambayi kansa disbelievingly. Sun d’au tsawon minti biyu suna kallon juna sannan daga bisani Anas ya kawar da kallonsa daga gareta ganin hawaye sun soma ambaliya mata a fuska. “Flower tashi mutafi.” Dagangan tace, “Habeebi ban gama chi bafa.” “Nasani zanje in siya miki wani lets leave now” yayi maganar tare da miqewa, kafin Fannah ta sake samun daman magana Anas ya d’agata badan tanaso ba tasoma binsa sunzo daidai bakin k’ofan kenan zasu wuce Ummimi tasa hannu ta tare Anas ta hanyan rik’o hannunsa chak! ya tsaya ba tare da ya juya ya kalleta ba. “Anas dan Allah karka min haka nasan banida iko akanka nasan banida daman tambayar yafiyanka amman dan Allah kabani daman baka hak’uri dan Allah Anas” ta k’are maganar cikin sautin kuka. Shiru Anad yayi totally speechless ayayinda zuciyarsa ke raya masa kar ya kuskura yabata wannan dama zuciyan nasa kuwa yabi ya fisge hannunsa daga nata yakama tafiya, dawani erin force Fannah taja kanta baya tare da k’wace hannunta dake a nasa cike da tashin hankali ya juyo yana kallonta. “Flower lets go!” Yayi demanding. “No Habeebi I’m not going anywhere with you se inhar ka tsaya ka saurari Ummimi, haba mana Habeebi wannan fa mahaifiyarka ce ita ta tsuguna ta haife ka bekamata kana wulaqantata kamar kashi ba, Habeebi nasan kanason Ummimi please give her this one chance to explain herself please for Hanan.” Alokaci d’aya Ummimi taji tana son Fannah dan yadda ta burgeta, “nagode ‘yata, Anas dan Allah kaji maganar matarka kabani daman baka hak’uri dan Allah Anas.” Hannunsa Fannah ta rik’o a hankali tana mirzawa “kaji Habeebi? Zaka iya bawa mahaifiyarka daman baka hak’uri, can you? Please...” Kallonsa ya miyar kan Ummimi daba abinda take banda kuka yana ganinta kawai se last incident daya faru tsakaninsu ya soma masa yawo a k’wak’walwa seyaji he can’t give her the chance she is asking for, gabad’aya ya riga ya dawo daga rakiyarta da ace 15years back ta dawo da yayi accepting nata amman banda yanzu. “No I can’t Flower I can’t mutafi nace!” Yayi maganar a tsawace. “Habeebi is okay calm down okay? Calm down” tayi maganar cikin salon dake kwantar masa da hankali. _*“INA TARE DA KAI Hanan NA TARE DA KAI*_do this for me please just listen to her” badan yanaso ba ya gyad’a mata kai. **** Zaune Anas da Fannah ke kan wani d’an dogon kujera a yayinda Ummimi ke zaune opposite them fuskarta jik’ap da hawaye. Cikin kuka ta soma magana; “Anas nagode daka bani wannan dama nagode sosai Allah maka albarka” ko kallon direction nata baiyi balle yace ameen. “Nasan banida izinin da zan fara rok’ar gafararka saboda abinda na muku, bansan ta ina zan fara baka hak’uri ba wallahi barin ku danayi shine babban kuskuren dana tafka a rayuwata Anas, kuskuren da har a yau ina nadamar sa kuma har in mutu zan cigaba dayi, wallahi sharrin shed’an ne it wasn’t my intention to leave you guys my family.” Ta tsaya ta share hawayenta tare da jan hanci “Anas I love you, wallahi ina sonka fiye da yadda nakeson kaina, tun tafiya na a kullum da tunaninka dana mahaifinku dakuma na k’annenka nake kwana nake kuma tashi dashi, da abinda na muku tun aduniya na fara ganin sakamakon sa ina ace na tafi lahira ban nemi gafararku ba? Anas dan Allah kayi hak’uri, baka bani dama ba amman ni na baiwa kaina kayi hak’uri ka yafemin please na tuba Anas ka tausaya min mahaifiyarka dan Allah d’ana barin iya samun kwanciyan hankali ba har se in ka yafemin ka tausaya min please.” Ta rushe da kuka miqewa Fannah tayi takoma gefenta ta tsaya tana shafa bayanta cike fa tausayi idanunta itama sunyi jazir. “Ummimi please kibar kukan haka nan ya isa dan Allah.” ‘‘Yata dan Allah kimasa magana ya tausaya min ya yafemin.” “Anas Habeebi ka tausayawa mahaifiyarka please.”Kai ya girgiza cike da takaici “mahaifiya? Yanzu ke Ummimi bakiji kunya ba da kike kwatanta kanki da mahaifiyata nikuma da d’anki? Bakiji kunya ba? As far as I’m concerned Ummie itace mahaifiyata. D’an da kika tunkud’esa kamar kashi 15 years ago, d’anda kika k’yamata d’an da kika masa permanent tabo a hannu” ya yi rolling hannun shirt nasa ya nuna mata tabon tabbas ta tuna itace taji mai ciwon danko kafin ta fice daga gidan taga yadda hannunsa ke yoyon jini amman saboda yadda shaid’an yafi k’arfinta alokacin ta fice ta barsa. Wani sabon kukan ta rusheda. “Kin tuna ciwon?” Ya tsamota daga duniyar tunanin data fad’a. “You think you still have the right to call me your son? Kinsan kalan k’uncin rayuwan da mukayi witnessing bayan tafiyarki? Kinsan ya akayi aka girmar damu aka girmar da Amal jaririyan da kika turo bayan tafiyarki precisely? Kinsan ya aka tarbiyyattar damu?” Zuciyanta taji yawani buga tare da sarin da kanta ke mata tana me k’ara tsanan kanta. “Kinsan ya akayi muka taso ba gatan uwa har muka fara mancewa da labarinki? Kinsan dare nawa muka kasa bacci saboda tunanin ki? Kinsan kwana nawa na d’iba inayi a waje ina tunanin ko zaki dawo mana? Kinsan what hell you made Abuu went through? The answer is No baki sani ba saboda alokacin kina chan da sabon mijinki kina more rayuwa. Its all over Ummimi I’ve loved you, we’ve loved you so dearly bu not anymore banida gurbin da zan sake ajiye soyayyan ki a zuciya na saboda na dawo daga rakiyarki, ke kika haifeni I can’t change that amman abinda nakeson kisani shine ki sa a mind naki baki tab’a haifan d’a me suna Anas ba, so nake ki mance dani kamar yadda na manta dake a rayuwa na cause I can‘t forgive you I will NEVER forgive you.” Yana kaiwa nan ya miqe da sauri tare da juyawa gudun kar hawayen dayake maqewa su fito seda ya shanyesu sannan ya juyo alokacin kuka sosai Ummimi ke wane zata cire ranta ayayinda Fannah ke bata hak’uri. “Anas tabbas ba k’arya cikin kalamunka tabbas nasan namuku laifi, laifin da yayi babban tabo duka a zuqatanku wallahi nayi nadama Anas kabani dama in biyaka 15years that passed, let me make it up for the past 15years da mukayi ba tare ba please kar ka hanani performing obligation d’ina as your mother.” “You are not my mother so you don’t have to saboda I don’t need you ko ayau akace Ummie wacce ta girmar dani wacce nake regarding nata as my mother ta rasu zan cigaba da rayuwa na balle ke, because I’m a grown up now as you can see I’m married saboda haka I don’t need you na yafe miki tsawon 15 years da mukayi ba a tare ba, ba sekin biyani ba, kitafi ki koma inda kika fito banasonki a rayuwa. Flower lets go” yaja hannunta suka soma tafiya, k’ok’arin jan hannunta daga nasa take amman takasa har seda suka isa mota tana kuka tana mai magana “haba Habeebi ban tab’a sanin your heart is as cold ba se yau, mahaifiyarka ce fa your own mother koda laifin kisan kai tayi be kamata ka mata haka ba, ka duba yadda tayi nadama mana kodan haka baraka saurara mata ba?” “Yes Flower barin saurara mata because I don’t need her 15years danayi ba ita yasa na mutu ne? No saboda haka bana buk’atar ta taje tasamu family’nta we don’t need her.” “Hab-” katsesa yayi “enough okay?!” Yayi maganar cikin sautin tsawa ganin yadda ta firgita sekuma yaji ba dad’i hannayensa ya aza kan shoulders nata “Flower I’m sorry banason ina miki tsawa, banason muna musu banason Ummimi ta zama sanadin samu fad’an da bama yi please stop crossing me kibarta let her be kinfi kowa sanin kalan k’uncin data jefa mu especially me, data tafi ta barmu without turning back. Ko kin manta saboda ita nasoma shaye shaye har ya kaiga nayi raping naki Flower duk kin manta? It because of her you suffered itace silan komai Ummimi batada advantage se disadvantages.” “Tabbas ba k’arya cikin maganganunka Anas” cewar Ummimi dake tsaye some inches away from them da alamun ta saurari dukkannin abinda Anas ya fad’a. “Tabbas duk wani abin haramun da ka aikata nima me laifi ce kuma nice sila saboda da ace ina nan da na hanaka aikata hakan, kayi gaskia da kace banida advantage se disadvantages all am asking for is kabani dama to be a mother to you again Anas koda baraka yafemin ba kabani dama insake rik’eka a hannayena in dafa maka abinci this is all I ask Anas please.” “You should hace thought about this 15years ago kafin kika tafi, alokacin ne wad’annan kalamu naki zasuyi tasiri akaina amma banda yanzu da kika riga kika karya min zuciya in baki sani ba kisani I’m not the Anas you left 15 years ago wannan Anas bayida tausayi saboda tafiyar mahaifiyar sa yakoya masa rashin tausayi da imani, my heart is as cold as stone dan haka kibar b’ata yawun bakinki kina bani hak’uri barin tab’a hak’ura ba Flower lets go.” “Okay Habeebi zan bika amman please kabani koda minti biyu ne inma Ummimi magana kaji?” “Flower me zakice mata? Kibarta please.” “Habeebi dan Allah fa nace please minti biyu kad’ai.¢ Kai kawai ya gyad’a mata “thank you so much my Lion.” Wajen Ummimi ta nufa taja hannunta suka b’ace daga kallon Anas bisa wani bench suka zauna Fannah na sharewa Ummimi hawaye. “Please kibar kukan hakanan ya isa dan Allah.” A raunane ta d’ago idanunta tana kallon Fannah “ ‘yata ya sunanki?” “Fannah, Fannah suna na.” “Masha Allah Fannah nagode da kulawarki a gareni Allah sak’a miki da alheri yakuma sauk’eki lafiya” (agarin share mata hawaye da Fannah ke hijabinta ya d’agu anan ne Ummimi taga cikin nata.) Mamaki ne ya mamaye fuskan Fannah taya Ummimi tasan tana da ciki? Cike da kunya tace, “ameen Ummimi please kibar kukan haka nasan Anas haka yake yanada taurin kai ne kuma sonki da yake yasa yake treating naki haka amman in shaa Allah wataran se labari Anas ze yafemiki nan bada jimawa.” “Haka kike gani ‘yata Anas ze iya yafemin abinda na masa?” “Allah ma muka mai laifi ya yafe mana balle d’an da kika haifa? Trust me ze yafe miki kidage da addu’a kawai nima zan saki cikin nawa.” “Nagode sosai ya Shettima yake dan Allah?” “Shettima nanan girmansa kusan d’aya da Anas yana kan karatu.” “Masha Allah nasan da kunya ma in tambayeki ya baby’n dana turo musu da ita bayan tafiya na wanda ko halittan fuskarta ban k’arewa kallo ba.” “Amal? Amal sunanta she is 15 years now itama ta na nan lafiya tana ss2 kinsan wani abu?” Kai Ummimi ta kad’a “sautin muryanku d’aya dakika fara min magana na zata ma Amal ce.” Murmushin takaici ta saki “Allah sarki Amal Allah yi mata albarka” “Ameen barikiga pictures nasu” nan taciro wayarta tana gwada wa Ummimi, hawaye sosai Ummimi ke kamar ba gobe tana me sake tsanan kanta abinda ta ma family’nta. “Amal da Anas sak kaman ni na, Shettima ma ba laifi, ‘ya‘yan Albarka Allah ya cigaba da raya min su yamusu albarka, yamuku albarka gabad’aya” tafad’a tana share hawayenta. “Ameen Ummimi.” “Ya Babansu yake? Wace Ummie da Anas yake fad’a kuma?” “Babansu na nan k’alau, Ummie k’anwar mahaifinsu ce.” “Ohhh Allah sarki nako ganeta itace ta girmar dasu?” “Eh itace.” “Allah sarki Allah ya saka mata da alheri, Babansu be sake aure ba?” “Gaskia be sake ba” “Allah sarki Ya Ibraheem, Fannah awani gari kuke yanzu da zama?” “Dukan mu a Maiduguri muke.” “Okay kunzo nan shaqatawa ne?” “Eh munma kusa komawa zaman nan ya ishemu gida yafi dad’i.” “Hakane ‘yata no place like home, dan Allah kitayani ma Anas magana nasan yana jin magananki koda bare yafemin ba yabani izinin zama mahaifiyarsa again, I want to make up for the past 15 years da mukayi ba a tare ba.” “In shaa Allah Ummimi karki damu sede wani gudu ba hanzari ba am sorry to ask mesa kikesa uniform na cleaners?” Murmushin takaici ta saki tare da share hawayenta. “Anan nake aiki Fannah as a cleaner.” “Subhanallahi cleaner kuma Ummimi? Meya faru? Meyasa?” “Long story ‘yata da wannan aikin kad’ai na dogara.” “Ummimi ina mijniki da ‘ya‘yanki? A yadda Anas yabani labari aure kikayi bayan tafiyanki.” “Tabbas aure nayi, Fannah mijin dana aura d’an cult ne nagudu nabarsa har a yau nemana yake.” “Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un to ‘ya‘yanki fa ko babu?” “Akwai har uku nafarin mata ne twins Basmah da Barrah sekuma autan Aleeyu wanda yake nan sak Anas har blue eyes nasu wanda sukayi inheritting dagu gun mahaifin kakana iri d’aya.” Hannu tasa a aljihunta taciro picturen ta nuna wa Fannah. “Woww masha Allah kyawawa dasu.” “Barrah da Basmah are 13 years, Aleeyu kuma 10 daganan ban sake haihuwa ba.” “Ayyah, wallahi Aleeyu sak Anas inda bansani bama cewa zanyi Anas ne haske kawai Anas ya d’ara sa kad’an but Ummimi a ina suke su yanzu? Suna wajenki ne ko wajen mahaifinsu?” “Ko d’aya ‘yata suna wajen mahalicinsu.” Tasa hannu tana share hawayenta. “Ban fahimce kiba Ummimi.” “Babansu yayi kud’i dasu Fannah, ya siyar da ‘ya‘yan cikinsa wa k’ungiyansu.” “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un!” take itama Fannar tasoma kuka. “Ummimi I’m so sorry kiyi hak’uri dan Allah, Allah sa k’arshen wahalansu kenan Allah sarki kiyi hak’uri dan Allah.” “Bakomai nima abinda yasa na gudo na barsa kenan saboda nice next target nasa jini na ne next abinda k’ungiyansu suke buk’ata dana gano hakan na gudu na barsa.” “I’m so sorry Ummimi shi rayuwa haka yake kowa da kalan jarabawarsa, ki cigaba da musu addu’a bale ma yara ne dukansu Allah sa masu cetoh ne.” “Ameen ya rabb-” bata samu daman k’are maganan ba ganin Anas datayi. “Flower lets go.” yayi i terrupting nata. “Toh Anas ina zuwa yanzun nan” bayan daya koma ta dawo da kallonta kan Ummimi. “Ummimi yanzu a ina kike kwana?” “Anan a d’akin da aka tanadarwa cleaners.” “Subhanallah mesa baki fad’a min ba? Bari zanyi wa Anas magana inshaa Allah zaki biyomu gida.” Hannunta Ummimi ta rik’o da sauri “a’a Fannah karki ma b’ata yawun bakinki please I don’t want to be a burden ni abinda nakso kimin d’aya ne hanyan da zesa Anas yayi accepting d’ina as his mother.” “Duka biyu zanyi Ummimi bareyi kina kwana agidan cleaners ba bayan da gatanki ina zuwa” nan ta fice taje tasamu Anas dake tsaye gefen motansu yana jiranta seda ta iso gab dashi ya saki mata murmushi wanda itama ta miyar masa “lets go?” Kai ta gyad’a masa tare da ajiye masa picture’n su Basmah akan bayan motar. “Meshi?” Ya tambayeta. “Ka duba kaga” ba gardama ya d’aga hoton yana kallo. Be sansu ba amman seji yake kamar yasansu gakuma me kamanninsa dayake gani cikin hoton harda blue eyes d’inma, tunaninsa ne ya jagule alokaci guda he seems puzzled. “Flower suwaye wannan? Waye wannan yaron?” “Kaga kuna kama koh?” “Sosai kuwa the eyes the face everything please suwaye ne?” “Your siblings Habeebi, k’annenka ne.” “K’annena?” Ya d’ago kai yana kallonta cike da mamaki. “Inada k’annen da sukafi Shettima da Amal ne?” “Yes step siblings naka ne.” “You mean yaran Ummimi?” Seta gyad’a kai pucture’n ya miyar mata “gashi banason ganinsu.” “Ayyah Habeebi basu maraye bale kace haka.” “What do you mean?” “Dukan su nan Allah yayi musu rasuwa, babansu your step-father d’an cult ne ya siyar da yaransa wa k’ungiyansu bayan nan yadawo kan Ummimi dalilin dayasa ta gudo tabarsa kenan har kaga take aiki anan ayanzu haka batada wajen kwanciya, Habeebi ka tausaya mata please...” *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [13:00, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 9⃣2⃣ Tunaninsa yaji ya katse kwatsam! sam yakasa yarda da abinda Flowersa ke ce masa, cikin sauti me rawa yayi maganar “Flower what did you just say?” Sake nanata abinda ta fad’i tayi. “Subhanallah! Flower are you sure?” Yayi maganar tare da karb’e picture’n yana sake kalla. “Kina nufin dukansu nan basuwa nan yanzu?” “Yes Habeebi” ta yi maganar tana gyad’a kai. “Allah sarki... They are in a better place in shaa Allah.” “Toh Habeebi Ummmi fah?” “Meh had’i na da ita? Infact ni banma yarda ba who knows ko duk k’arya take tanason in tausaya mata ne tayi coming up da plan d’innan.” ”Haba! My Lion don’t be like that, taya zakace haka wa mahaifiyarka? Inhar k’arya kake tsammanin tamana uniform na cleaners dake jikinta kad’ai sheda ce, Habeebi mahaifiyarka cefah feel sympathy towards her atleast yara uku fa ta rasa one, two, three” ta irga da hannunta. “Toh Flower laifi na ne? Nine na siyar mata da yara? Kwad’ayinta ya kaita kinga erin disadvantage da nake fad’a miki ai yanzu itace silan mutuwan yaran nan, mschw! What a pity.” “I know Habeebi bara mu iya canja komai ba abinda ya faru ya riga ya faru please ka taimaka wa Ummimi.” “In taimaka in mata meh?” “Mutafi da ita hotel da muke.” D’an dariyan rainin wayo ya saki “intafi da ita? LOL lallai kam Flower you are such a wonder ni magananta ma ya isheni kimiyar mata da photo d’in ki taho mutafi.” Haka Fannah ta riga lalashinsa tana basa hak’uri da k’yar d’in k’yar ya yarda Ummimi ta bisu amman ba’a cikin motarsa ba hakan kuwa akayi. Bayan taje ta taho da Ummimi ta tsare mata cap (taxi) kafin Ummimi tashiga taje gun Anas dan masa godiya, yana zaune cikin mota yana jiran Fannah. “Assalamu Alaikum Anas nagode da taimakon dakamin, Allah saka da alheri ya kuma maka albarka.” Tayi maganan tana tsaye ta bakin windon side na Anas. Ko kallonta beyi ba se latsa wayansa yake chan yace, “thank her not me bani na taimaka miki ba excuse me please” Shiru tayi bata kuma cewa komai ba takoma taje ta shiga cap d’in hawaye na bin k’uncinta har suka isa hotel d’in kuka bata bar kukan ba. Bayan isansu Fannah ta kalli Anas sannan cikin salon da inta mai magana yakeji tace, “My Lion nace zakayi wa Ummimi booking room koh?” Tayi maganan tana murza hannunsa a hankali. “Flower kinga ba haka mukayi dake ba cewa kikayi zata biyomu nan bakice zan mata booking room ba saboda haka figure out me zakiyi da ita” yana kaiwa nan yafito daga motar ya wuce ciki. Binsa da kallo tayi “Habeebi yau ko kafi babarka k’ok’ari seka mata booking room d’innan” ta fice daga motar ta sallami taxi driver’n. “Ummimi muje reception ki zauna achan kafin amiki booking room.” “Nagode ‘yata Allah miki albarka.” “Ameen Ummimi” anan tajata zuwa reception daidai zata juya Ummimi ta riqo hannunta “Fannah karki b’oye min Anas yace bare kama min d’aki bakoh?” “A’a Ummimi ya kike magana haka-” katseta Ummimi tayi “please karki min k’arya” zama Fannah tayi a gefenta hannunta riqe cikin na Ummimi. “Inason kisa a ranki Anas ze yafe miki saboda mahaifiyar sa ce ke kinji?” Kai Ummimi ta gyad’a mata “good kuma please kukan ya isa haka zan masa magana ina zuwa” ahaka suka rabu. **** Miqe Anas ke akan gado da newspaper a hannunsa yana karantawa yana jin k’aran bud’e k’ofa ya ajiye yasoma baccin k’arya agefensa ta zauna “My Lion nasan ba bacci kake ba.” Shiru yayi be tanka taba. “Habeebi katashi please kaji?” Ta hau jijjiqa sa badan yanaso ba ya bud’e ido. “Meh?” “Habeebi Ummimi mana kamata booking room.” “Banida kud’i.” “Youngest billonaire d’in? Habeebi please ka tashi” nan ta miqe ta hau jansa daga gadon sam takasa murmushi ya saki sannan yajata ta fad’a jikinsa. K’ara ta saki sosai sanadin cikinta data buga. “Arghhh! Habeebi ciki na.” “Sorry Mom Hanan” ya zaunar da ita kan cinyansa. Kukan k’arya ta soma tana riqe cikinta. “Flower nayi hitting naki sosai ne?” Kai ta gyad’a tana murzq idanunta. “Am sorry kinji? Muje asibiti?” “A’a nikayi booking wa Ummimi d’aki.” “Flower barinyi ba.” Rushewa takumayi da kuka, “Flower wai bara kibar kukan nan ba?” Ta gyad’a kai ba yadda beyi tayi shiru ba amman taqi daga k’arshe seda ya yarda da k’udirinta. “Okay, okay naji zan mata for Hanan’s sake.” Koma meh tace a zuciyarta tare da share hawayen k’aryan nata. Tana ganinsa ya fice ta saki murmushi. Nan da nan ya sauqa yaje yama Ummimi booking d’aki a chan last floor ta yadda bare ma na kallonta ba bale yana jin baqin ciki. Tana zaune a reception d’in Anas yazo ya wuceta batareda yace mata ko k’ala ba bayan daya gama komai ya nufo inda take tare da ajiye mata key d’in a kujerar dake gefenta “room 116” kad’ai yace da ita. Hannunsa ta riqo kafin ya kub’uce mata. “Anas nagode Allah saka maka da alkhairi.” Hannunsa ya fisge ba tare da yace da ita komai ba. “Anas dan Allah kayi hak’uri kamin magana barin iya jure fushinka ba please talk to me your mother” ba tare da yace da ita komai ba ya haye sama d’akinsu da Fannah. ***** Haka nan tun daga ranan Ummimi tasoma zama dasu Fannah ko kad’an Anas baya shiga harkarta magana ma ba mata yake ba, koda ta mai magana baya amsata ba yadda Fannah batayi dashi ba amman yak’i yafewa Ummimi, a dalilin haka tasoma tashi Sallan dare tana roqan Allah. Cikin d’an k’ank’anin lokaci Fannah suka shaqu da Ummimi dan yadda Fannah kebata kulawa tamkar uwarta abinci kullum ita ke kai mata dan kuwa tsoron placing order ma take, haka Fannah tasa Anas agaba seda ya siya wa Ummimi kayan sawa da sauran abubuwan da zata buk’ata. Dukda shariyan da Anas ke mata hakan be hanata yimasa magana anytime she gets the chance to ba fatanta Allah sa Anas ya bata daman da take nema. Sunyi zaman two weeks tare Anas ya fara zancen komawa gida, Nigeria badan komai ba dan ya rabu da Ummimi. _4:30PM_ Yana cikin harhad’a musu kayaki kasancewar gobe zasu tafi Fannah ta shigo d’akin bayan fitowarta daga d’akin Ummimi, akan gado ta zauna “sannu da aiki Habeebi.” “Yauwa Flower.” “Uhm nace in zamu koma Ummimi zata bimu ba?” Barin abinda yake yayi “waze bi wa?!” Yayi maganar cike da rashin yarda. “Ummimi zata bi FAHNAS nace.” “Humm!” yaja numfashi “sede in wani FAHNAS d’in kam ba wanda nasani ba.” “Toh My Lion ita kad’ai zamu bari anan ne?” “Dama dawa muka sameta? Ita kad’an ta muka sameta haka kuma zamu barta” “Haba! My Lion katuna fa batada family yanzu we are her only family.” “Flower I’m not her family kuma ba inda zanje da ita ta sake messing min family like she did before.” “But Hab-” “Period!” Ya katse ta. Bata sake ce masa komai ba gudun kar suyi fad’a. Chan bayan sallan isha bayan sun k’are chin abinci ta matso ta zauna kusa dashi akan gado tare da riqo hannunsa cikin nata. “Habeebi please badan niba dan Allah kar kabar Ummimi anan baka tunanin in rananda step father’nka ya ganta ze siyar da ita kamar yadda ya siyar da su Barrah? Baka tunanin barinta anan had’ari ne Habeebi? I’m not asking you to forgive her all am asking is mutafi da ita kar mu barta anan please Habeebi don’t say no please.” Shiru yayi harga Allah bai tunanin ze iya ce ma Flowersa no this time akan abinda yasan ba gagaransa zeyi ba sede yanzu in yabar Ummimi tabisu dole gida ze kaita abinda bayyaso kenan yafison kamar yadda suka saba ba ita su cigaba da kasancewa ahakan shi bama wannan ba mezece wa Amal da batasan tanada wata mahaifiya ba bayan Ummie? Abinda ke damunsa kenan. “Habeebi please kayi hak’uri mutafi da ita kaji?” Kai zallah ya gyad’a mata yana me nazarin aina ze kai Ummimi bayan isansu Nigeria. “Thank you so much My Lion” tayi pecking nasa tare da miqewa. “Ina kuma zakije Flower?” “Zanje ince ma Ummimi ta shirya kayanta zamu tafi gobe.” “Flower shine baraki iya kiranta a waya ba? Ni banason kina unnecessary zirga-zirga kinde sani bakida lafiya kuma munada tafiya gobe.” “Don’t worry Habeebi I won’t take long” tayi mai blowing kiss, murmushi ya mata sannan ta fice. Zaune ta tarar da Ummimi kan gado as always ta had’a tagumi bayan tayi sallama ta shigo tazauna a gefenta. “Ummimi ki shirya kayanki zamu tafi gobe.” Cike da rashin fahimta ta d’ago kai tana kallonta “ina zamuje Fannah?” “Nigeria! Zakije kiga su Amal!” ta sanar da ita cike da jin dad’i. “Nigeria?! Kina nufin Anas ya yarda zan biku? “Ai na fad’a miki Anas na sonki he is just taking time to adjust nan bada jimawa zakuyi sorting out komai.” “Allah sa Fannah nagode kuma sosai Allah biyaki.” “Ameen Ummimi ba komai tashi mu shirya miki kayan naki.” “A’a please karki damu kayan nawa dududu nawa ne? Keda bakida lafiya ma kije ki huta dan Allah kar gajiyan ya miki yawa.” “Tunda haka kikace fine kiyi ki shirya ki huta kema Allah kaimu gobe.” “Ameen nagode kima Anas godiya please nasan koda mutuwa zanyi ina mai magana ba amsani zeyi ba.” “Bakomai Ummimi zan masa in shaa Allah seda safe” ta rufo mata k’ofar. **** Bayan Anas ya kashe musu wuta suna kwance kamar yadda suka saba Fannah ta kira sunansa, “Habeebi.” “Yes Flower.” “Thank you so much for everything.” Ta fad’a tare da sake shigewa jikinsa. “You don’t have to thank me Flower, ma godiyan me kike?” “Aika fini sani d’azu Mami takirani tace in maka godiya mekayi musu, nayi nayi da ita ta fad’amin tak’i.” “Haha!” yayi dariya kad’an “hakane?” “Eh mekayi musu?” “Babu.” “Kamar ya babu Habeebi duk alkhairun da kake musu da a baya Mami bata tab’a cemin na maka godiya kamar na yau ba meh ka musu please?” “Nace miki babu lets sleep tomorrow is a big day.” “O’o ni seka fad’amin wani alkhairi kamusu.” “Nace miki babu please kiyi bacci ko Hanan ma zata samu tayi, goodnight” yayi pecking kanta. Shiru tayi chan ta kira sunansa “Habeebi.” “Yes Flower lets sleep.” “Thank you kaji? Allah k’ara bud’i.” Magana yake cike da gyangyad’i “Flower nace miki banason godiyan nan.” “Bakasan akan mefa nake maka godiyan ba.” Ya nisanta “akan meh?” “Ummimi ce tace na maka godiya.” Shiru yayi bece komai ba. “Kaji My Lion?” Nan ma shiru data d’ago kai ta kallesa setaga idanunsa a rufe she is sure ba bacci yake ba, bayason maganan Ummimi ne. “Liar nasan ba bacci kake ba kadeji Ummimi tace ta gode” nanma bece komai ba murmushi ta saki tare da jan hancinsa. “Awwch!” Ya sakar da k’ara “kinsan da zafi koh?” “Aww! kana jina kamin shiru kenan.” “Sa’an ki d’aya Baby Hanan if not da na rama.” Gwalo ta saki masa sannan yajata jikinsa suka kwanta*** _washegari..._ As early as possible suka shirya luggages nasu duk na acikin mota Anas yabari asa akwatin Ummimi a motansu yak’i taxi aka tsare mata ta shiga ciki, kusan a tare suka isa airport akayi musu ciki da akwatinansu. A sama su Fannah suke a yayinda Ummimi ke k’asa ita kad’ai ba yadda Fannah batai da Anas yabar Ummimi ta samesu ba yak’i. _2 hours later..._ Miqe Anas yake kan wani medium sized bed se baccinsa yake sha ayayinda Fannah ke zaune a d’ayan side d’in da Qur’ani a hannunta se karatu take tayi daidai takai inda k’arfinta ya k’are ta tsaya tare da miqewa ta sauk’a k’asa gun Ummimi as always ta sameta ta ta had’a tagumi bayan ta zauna a gefenta ta dafe kafad’arta se anan Ummimi tasan da shigowarta. “Fannah” takira sunanta a bit suprised. “Na’am Ummimi kin zauna shiru ko TV ne ki kunna mana.” “A’a barshi karki damu, ya Anas yake?” “Yana bacci kema ya kamata ki kwanta.” “A’a nikam, se hankali a kwance ake iya bacci ai.” D’an murmushi Fannah ta sakar mata “toh ga Qur’ani ki karanta” ta miqa mata. “Nagode kema kije ki huta wannan hawa da sauqan ze dameki kinga already k’afafuki sun kumbura.” “Toh Ummimi.” “Nace yaushe ne jikan nawan ze fito?” D’an dariya ta saki dan kunya ma takasa fad’a mata. “Surikar tawa tana jin kunya na ne?” Ummimi tayi teasing nata. “Nanda wata uku in shaa Allah.” “Ahh ashe ma kin kusa toh Allah raba lafiya ‘yata Allah ya sauk’eki lafiya.” “Ameen Ummimi nagode barinje in huta nima.” “Yawwa ‘yata” ahaka suka rabu beside Anas taje ta kwanta alokacin har ya tashi. “Flower ina kikaje?” “Gun Ummimi.” “Baraki koyi zama gu d’aya ba ko kinga k’afafunki kuwa? Wai bakiya jin tausayin kanki ne?” “Habeebi please ya isa ai dama kumburin dole ne kaide kace kanason min surutu ne saboda gun Ummimi naje inda toilet nace na shiga ai barakayi magana ba.” “Ohkayyyy haka kika ce? Toh har mu isa banason kisake sauk’a wajenta am not asking you am ordering you as your husband.” “Sekayi ai” tayi maganar k’asa k’asa. “Kuma najiki nide na fad’a miki.” Baya ta juya masa ba tare da tace komai ba haka tundaga nan bata sake masa magana ba kodaya tasheta Sallan Azahar haka La’asr ma shima be mata magana ba. 10 hours ya d’aukesu sannan suka iso Nigeria inda suka sauk’a a Sandralia Hotel Abuja har anan Fannah bata sake ma Anas magana ba, ruwa ta watsa taso shiga duban Ummimi amman Anas ya hanata. Bayan ta shirya cikin kayan baccinta ta zauna kan gado tana ma kanta tausa a k’afafunta, fitowan Anas daga wanka kenan singlet da nickers yasa ya hauro gadon yana k’are mata kallo. “Flower.” Shiru tayi bata tanka sa ba. Kusa da ita ya matso “Flower bara kimin magana ba?” Nanma shiru se massaging kumburarrun k’afafunta take hannunta ya d’aga daga kan k’afan nata nanma bata ce masa ko k’ala ba. “Flower wai barakimin magana?” Nanma shiru. “Okay I’m sorry kinji? I’m sorry.” “Kasakemin hannu as you can see am massaging my legs.” “Flower I said I’m sorry.” “Naji sakeni toh.” “Bari zan miki.” “Banaso zanyi abuna da kaina.” “I’m sorry” ya sake hannun nata tare da kama kunnuwansa ko kallonsa batayi ba ta cigaba da massaging k’afanta. “Flower please.” “Wai hak’urin me kake bani? Nace kamin laifi ne?” “Baki fad’a ba amman nasan na miki laifi and I’m sorry kije kisameta in kinaso.” “Banaso” ta fad’a stubbornly. “Yi hak’uri mana Mom Hanan” ya sake matsowa kusa da ita closing the gab between them, gashin kanta data barbaza a kafad’anta yahau shafawa. “Yi hak’uri kinji barin sake ba.” Kallonta ta miyar garesa “I’m sorry sweetheart” d’an murmushi ta sakar masa ma’anan ta huce. “Thats my woman!” Lips nata yasoma laluba bata hanasa ba se dab da bakinsu ya kusa had’iye tasa hannu ta kama mai baki “no kisses today thats your punishment” tayi maganar tare da miqewa daga kan gadon ta sanya hijabinta. “Oh common please Flower ko peck ne.” “Nace NO! Gobe zaka sake repeating abinda kayi yau.” Tana kaiwa nan ta fice zuwa d’akin Ummimi. Some minutes later ta dawo har anan Anas beyi bacci ba yana jiranta, a nitse ta cire hijabin ta haye gado ta kwanta ganin bata matso kusa dashi ba yasa ya matso dakansa tare da zama. K’afanta ya miqar kan cinyansa sannan ya fara mata massaging. “Ta nan ka b’ullo kenan? Saboda in ka gama in baka kiss as token of appreciation, uh-uh yau ba kiss na fad’a maka smart guy, wannan logic nakan bareyi aiki ba yau.” Dariya yaso yi dankuwa ta kamasa amman seya matse. “Ni ba haka nace miki ba am massaging your legs because I love to” “Humm! Allah sa de, nagode” bayan daya gama yaja d’ayan ma yamata godiya ta masa sannan ya kashe musu wutan ya koma ya kwanta agefenta yana wasa da gashin kanta duk wani salo nashi yayi applying amman Fannah tak’i bari yayi kissing nata haka yatayi har ya gaji seda tajishi yayi shiru sannan ta juyo tana kallon shi unexpectedly tayi pecking nasa a lips. Kafin ta d’ago kanta ya riqeta gagam yasoma sarrafata haka sukata romancing junansu har seda bacci b’arawo yayi gaba dasu. *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [13:00, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 9⃣3⃣ _washegari..._ Da safe Anas ya tashi yayi wanka sannan ya had’a wa Fannah ruwan ta itama tayi, dakansa ya shafa mata mai ya cire mata d’aya daga cikin had’ad’d’un maternity gowns nata tasa sannan suka karya. “Habeebi ya naga kana zipping mana akwati?” “Yes Baby zamu wuce Maiduguri yau ina zaki iya ko mu bari se gobe?” “No its okay with me toh baka sanar dani ba bale in fad’awa Ummimi, barinje in ce mata ta shirya.” Hannunta ya riqo da wuri “no Mom Hanan baramu tafi Maiduguri da Ummimi ba anan Abuja zan barta zan mata renting gida tayi zamata anan we don’t need her again.” “Haba My Lion wani erin magana kake haka? Ita da wa zaka barta anan?” “Ita kad’anta kamar yadda muka sameta ita kad’ai a NY ai dama cemin kikayi zamu dawo da ita 9ja bawai zata bimu gida ba.” “Oh Habeebi wallahi banajin dad’in abinda kakeyi ko kad’an banaso haba mana Ummimi fa mahaifiyarka ce ko kak’i ko kaso itace mother’nka baka iya canzawa.” “I know ba abinda zan iya thats why I need her out of my life.” “Wai meke damunka ne Baby? Nifa ba haka nasanka ba Ummimi is following us home.” “Sede in ke zaki biya mata kud’in jirgi which I’m not allowing you.’ “Fine karka bari zan kira Abuu in sanar dashi I’m sure shi ze biya mata.” “No Flower you are not doing that I forbid you to call him wai mesa kikeson muna fad’a ne? I’m your husband amman ko kad’an bakiya jin magana na, Ummimi is not following us and that stays that period!” Ya fad’a a tsawace tare da matsawa yakoma kan kujera ya zauna. Kuka ta tsaya tanayi a wajen chan takoma kan gado ta zauna se kuka take wanda ke mugun tayar wa Anas da hankali gani yayi kamar ze iya jure sautin kukan nata amman ina he can’t. “Flower wai baraki bar kukan ba?” K’ara k’arfin kukan nata tayi cike da tashin hankali ya matso kusa da ita yana aza hannunsa ajikinta taja da baya. “Flower kibar kukan mana wai ke bakisan its bad for your condition bane?” “Kai da kasani kuma kake sani kukan fah? Ni ka tashi min akai” ta juya masa baya. Gadon ya haye yadawo ta inda take fuskanta. “Ya isa toh I’m sorry Flower ke kike sani miki masifa nace miki banason zancen Ummimi amman bakiya ji sekita min maganarta. Kiyi hak’uri kinji? Kidena min magananta se baramuna samun midunderstanding ba.” Baki ta murgud’a mai “ni katashi min kuma barin iya tafiyan ba yau mara na naciwo.” “Toh naji sannu, se gobe zamu tafin kenan.” Ta gyad’a mai kai “kuma ni barin tafi ba seda Ummimi.” “Kingani koh?” “Toh Habeebi wani erin magana kake please?” Ta tashi ta zauna “taya zamu taho da ita 9ja kuma semu barta anan ita kad’ai ai gwara ma ace tun farko mun barta achan NY, ni gaskia in bada Ummimi ba barin bika ba.” “Se mu gani ai” daidai ze juya kenan tariqo hannunsa “Habeebi please dan Allah kayi hak’uri mu koma da Ummimi please Habeebi kamin wannan ka gama min komai Habeebi please don’t say no please please sweetheart, the father to my children please say yes kaji Baby? Say yes please.” Shiru yayi bece komai ba dawowa tayi ta zauna kan cinyansa “please Habeebi say yes kaji my Baby?” Nanma shiru “Sweetheart please...” “Toh inta bimun aina zamu ajiyeta?” “A gidan mu zata sauk’a for the meantime.” “A gidanmu? No barin kaita gidana ba never.” “Toh naji ba’a gidanmu ba, a gidanku nasan Abuu ze bata d’aki inbe bata ba ko gun Mami zan kaita please say yes Habeebi.” “Naji” amsar daya bata kenan. Hannayenta ta zagaye a wuyansa tare da pressing masa hot kiss “I love you Habeebi, I love you so much” tayi pecking nasa a kumatun damansa sannan a na hagu se tip na hancinsa “mufita sight seeing (ganin gari) yau kasan bansan cikin Abuja ba.” “As you wish Mom Hanan” yayi pecking lips nata “sa hijabinki muje.” “Yauwa Abu Hanan zamuje da Ummimi?” “Bansani ba in zaki tashi muje toh fine inkuma a’a muyi zaman mu.” “Dama wasa nake nasan ba yarda zakayi ba” daidai zata mik’e kenan Hanan tayi kicking. “Habeebi Habeebi! Hanan moved tayi motsi!” tasa hannunta daidai inda tajiyo motsin, shima hannun nasa yasa wajen kad’an kad’an sukejin motsinta nan da nan suka fita basu suka dawo ba se kusan Maghrib Sallah sukayi Fannah ta wuce d’akin Ummimi inda ta sanar da ita zasu wuce Maiduguri gobe. Hira kad’an suka tab’a Fannah tamata seda safe ta dawo d’akinsu anan suka kwanta da wuri kasancewar zasu hau hanya gobe. **** K’arfe 10:30AM su Fannah suka isa Maiduguri already driver na jiransu a airport, anan ma sam Anas yak’i barin Ummimi shiga motansa haka ta shiga taxi gidansu suka fara wucewa inda shida Fannah suka shiga suka watsa ruwa aka bar Ummimi cikin taxi tana jira, Fannah tayi tayi da Anas yabar Ummimi ta shigo ta watsa ruwa itama amman yak’i ba yadda ta iya haka ta hak’ura bayan sun sake shiri suka fito suka wuce gidansu Anas. Daidai gaban gate Anas ya tsaya bayan me gadi ya bud’e gate ya shiga, itako Ummimi a waje driver ya ajiyeta da kud’in da Fannah ta bata ta biya sa. Fitowar Fannah daga mota ta kama hanyan waje dan shigo da Ummimi ta soma tafiya kenan Anas ya tsayar da ita. “Flower where to?” “Zan shigo da Ummimi ne kafara shiga we will follow afterwards.” “Mschw! Wai ita batasan hanyan ciki bane da sekin shigo da ita? Ni kidena wahalar min da Hanan akan Ummimi.” “I’m sorry Babe yanzu zan shigo da ita ko zaka jira ni neh mu shiga tare?” “Mschw! You are trying me koh?” D’an murmushi ta sakar masa sannan ta fice a waje ta samu Ummimi. “Bismillah mushiga daga ciki Ummimi.” “ ‘Yata nace gidan da muka baro d’azu shine naku dana Anas?” “Eh Ummimi.” “Masha Allah gidan naku yayi kyau sosai kamar a ture wallahi.” “Kai Ummimi mungode Anas ne yayi desinging gidan da kansa kinsan architecture ne ayanzu haka shine CEO na Flames Enterprises one of the biggest Emterprise a Nigeria in whole, he is being referred to as Nigerias youngest billonaire, Ummimi ki godewa Allah Anas naki is very bright.” Hawayen jin dad’i ne suka soma gangaro wa Ummimi “Alhamdulillah! Oh! Allah sarki Anas Allah ya cigaba da mai bud’i ya kare shi daga sharrin maqiya, ameen.” “Ameen Ummimi mu shiga.” “A’a Fannah tukuna, ina ne nan?” “Nan gidansu Anas ne mushiga Abuu na ciki.” “Kina nufin wannan babban gidan na Abuun su Anas ne?” “Eh Ummimi” “Allah mai iko, me azirtawa dakuma talautarwa, Allah sarki ban kyauta wa kaina ba wallahi ko kad’an, da ace na k’ara hak’uri na cigaba da zama da Ya Ibraheem da atare zamuyi wannan arziki, Allah cigaba da masa bud’i yakuma rabamu da sharrin shaid’an gabad’aya.” “Ameen Ummimi mushiga.” “Fannah banida courage na shiga, ina tsoro nasan cikinsu ba wanda zeyi accepting d’ina sabida abinda na musu da ciwo zasu ce ban tashi dawowa ba sedana ga Ya Ibraheem yayi arziki, please ki kaini wani gun daban kokuma in zan iya tuna hanya in je gidanmu that is in iyayena suna raye.” “Ummimi just trust me kinji? Mushiga ciki please na tabbata idan duk sukaji labarin ki zasu yafe miki musamman ma Shettima I know him shi ze fara accepting naki” Hannu tasa ta share hawayen nata sannan tabi bayan Fannah hannunta riqe cikin na Fannah. Amal na bud’e k’ofa taga Anas ne tsaye jikinsa ta d’ale tana mai oyoyo! “Ya Anas I missed you so much, shine zaku dawo baku sanar dani ba tun shekaran jiya nake trying numban ka dana Ya Fannah basu shiga.” “Sorry Angel we wanted suprising you su Abuu suna ciki?” “Yes kowa na gida ina Ya Fannah da Hanan d’ina?” “Gata chan!” yayi mata nuni da yatsa. Tafe Fannah ke da Ummimi behind her. “Ya Anas ita da wa wancan?” “Nima bansan taba kinsan me nakeso dake Angel?” “A’a” ta girgiza mai kai. “Karki kuskura kimata magana kinji? Koda ta miki karki mata magana she is a bad person.” “Really Ya Anas? Mesa toh?” “Trust me kinji Angel? Karki kuskura kimata magana” Yayi pecking nata a goshi. Alokacin da su Ummimi suka gama k’arisowa Amal ta ruga tayi hugging Fannah har agarin haka ta bige mata ciki. “Amal kinason kijiwa Hanan naki ciwo ne?” “A’a Ya Fannah barin k’ara ba its just that I missed you wallahi gashi munyi hutu ba gun zuwa Ya Shettima kullum na cikin bullying d’ina.” duk maganganun nan datake bata kalli Ummimin da tayi mutuwan tsaye tana kallonta ba ko kyaftawan ido ba. “Aiko ga Ya Anas naki ya dawo seki kai masa k’orafi.” “Haha! Ai kibari Ya Anas yace ze rama min ko Ya Anas?” Tayi maganar tana k’ok’arin maida kallonta kan Anas a garin haka idanunta suka sauk’a kan Ummimi da idanunta suka ciko dam da hawaye ganin ‘yar data bari a cikin tsumma ne ta girma haka tazama babbar budurwa kuma kyakkyawa. Kallon cikin ido suka tsaya sunayi wa juna na kusan minti biyu, wani erin yanayin da Amal bata tab’a tsintan kanta ciki ba tasoma yau. Aina na santa? tambayar data ke tayi wa kanta kenan. “Amal” cewar Ummimi tana mata murmushin daya zame mata dole. Ta bud’e baki zata mata magana kenan seta tuna abinda Anas yace mata sekuma tayi shiru. “Amal barakiyi mata magana bane? Bakiji ta kira sunan kiba?” Cewar Fannah. “Baruwanki, bata santa ba taya zata mata magana zo Angel d’ina na siya miki iphone 7s ma taho kinji?” “Dagaske Ya Anas yeyy!” Taje tayi hugging nasa. “Ina yake Ya Anas?” “Nachan gida tare zamu koma yau zaki kwana mana ba?” “Yeyyy!!! Mushiga ciki toh” dake hankalin ta har a yanzu na yara ne anan ta mance da chapter’n Ummimi taja hannun Anas suka shige ciki. “Ummimi please karkiyi kuka dan Allah, nasan da akwai k’wararren dalilin dayasa Amal tak’i miki magana Anas ne ya hanata kuma jin maganansa take har fiye da yadda takejin na Abuu, duk abinda yace mata yi take but karki damu with time zaku saba she is fun to be with mushiga daga ciki.” Da k’yar tayi convincing Ummimi data kariya da reaction na Amal tabita suka shige ciki bakowa a parlourn illa Anas dake a dining space yana shan ruwa bayan ta zaunar da Ummimi kan kujera ta nufa inda Anas yake. K’asa k’asa take maganar ta yadda Ummimi barata jisu ba. “Habeebi yanzu abinda kayi ka kyauta kenan?” “Menayi kuma yanzu?” ya bud’e goran ruwan ze kai baki tasa hannu ta k’wace. “Ma tambaya na kake ko? Mena hana Amal yima mahaifiyarta magana?” “Haka Amal tace miki ni na hanata? Ma in ni na hanatan toh ina ruwanki? Tsakaninsu su biyu bata santa ba taya zata mata magana bani ruwana insha.” “Barin bayar ba.” “Ki riqe akwai wani cikin fridge d’in ai” daidai zebud’e kenan tasa hannu ta taresa. Murmushi ya saki “I will excuse you Flower saboda dama mata masu ciki sunada taurin kai.” pecking nata yayi a goshi wanda tuni ta tunkud’esa, killer smile nasa ya kashe mata “Shettima! Shettima!” Yau hau k’wala masa kira. Daidai nan Ummie da Abuu suke fitowa har Amal taje ta sanar dasu dawowan su Anas dawata mata me kama da ita da Anas harma da Shettima kad’an kad’an. “Oyoyo! Mutanen New York ne a gidan namu, maraba lale!” cewar Ummie alokacin data ga Fannah, hugging nata tayi ahankali gudun karta jimata ciwo anan sukayi exchanging greetings. Ummimi dake a parlour ba abinda take se kallonsu hawaye na bin k’uncinta. “Me kuke tsaye anan?” Abuu ya tambayesu. “Uhm ruwa nazo d’aukawa Anas” Fannah tamai qarya “gashi Anas” murmushi ya saki sannan ya karb’a. “Toh mu k’arasa parl-” be samu daman k’arisa maganan ba kasancewan ido hud’u da sukayi da Ummimi kwata kwata ya kasa amincewa da abinda idanunsa ke gane masa cewa ma yayi ko imagination nasa ne kawai, Ummie ma was at shock alokacin data ga Ummimi she couldn’t believe it either. Cike da rashin yarda Abuu ya juyo yana kallon Anas fuskarsa d’auke da son k’arin bayani har b’ari bakinsa ke. “A.. An.. Annas wac..wacce wancan?” yana nuna Ummimi da yatsa, shida Ummie suka kasa kunne suna jiran amsar sa. Daidai nan Amal ta falfalo da gudu, Shettima na biye da ita yana huci sanadin d’aukar masa cookies dayayi niyyan kaiwa Afrah da tayi. “Ai wallahi yau se jikinki yayi tsami, sa’an kine ni da zan ajiye abu ki d’auka har kichi?!”” Yayi maganar se binta yake a yayinda take ta gudu tana kiran sunan Anas “Ya Anas! Ya Anas! Shettima ze min duka.” Suna isowa dining area’n duka suka sa full stop tuni Amal tayi bayan Anas. Ganin Abuu Shettima ya dakata kaman ance ka juya ya juya idanunsa se akan crying Ummimi. Idanunsa ya zaro sosai kamar ze ciresu sam shima ya kasa yarda da abinda idanun nasa ke gane masa. “Abuu wace wancan?” Abinda ya iya tambaya kenan. “Ya Anas meke faruwa haka? Ya naga su Abuu sunyi shiru.” Amal ta tambaya. “Anas magana nake maka wacece wancan?” cewar Abuu. “Abuu Nima bansanta ba Flower keda kika kawo ta seki musu bayani” anan duk suka maido da kallonsu kan Fannah suna jiran amsarta seda ta kalli Ummimi sannan ta kallesu bakinta ya bud’u “Abuu wancan Ummimi ce, Ummimin ku.” *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [13:00, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💕* 9⃣4⃣ “Um... Waye?!”Abuu yayi maganar cike da k’in yardan abinda Fannah tace. “Eh Abuu Ummimi ce” ta sake tabbatar masa, juyawa yayi ya miyar da kallonsa a gareta “Aysha?” Yayi questioning nata hawaye ne ke ambaliya kan fuskarta “nn..na’am Ya Ibraheem” “Ummimi?” Cewar Shettima disebelievingly. “Na’am Shettima.” “Noo this can’t be wannan ba Aysha bace ko Nafeesa?” Abuu yayi maganar har yanzu be yarda ba. “Ya Ibraheem ka kwantar da hankalinka please ba shakka zahiri wannan Aysha ce.” “Meta kemin a gida? kice mata ta tashi tabar min gida tun kafin nakira mata securities banida wani alaqa da ita” yana kaiwa nan yayi ciki. “Ya Ibraheem ka tsaya please” Ummie tabi bayansa. Wani erin matsanancin kuka Ummimi ketayi abin tausayi ayayinda su Shettima suke kallonta kamar TV har a yanzu yakasa motsawa dan yadda mamaki ya ziyarce sa gabad’aya ashe dama ze sake sa mahaifiyarsa a ido? “Ya Anas wace ita? Dagaske kake she is a bad person shiyasa Abuu yace tafita mana daga gida?” “Yes Angel mushiga ciki in ta tafi se mu fito” Fannah ce ta dakatar dasu. “Anas baka gani is about time Amal tasan gaskia itama?” “Flower don’t you ever tell her a thing about it, am not asking you am ordering you banason kifad’a mata wani abu I hope am clear” yana kaiwa nan suka fice. “Shettima” Fannah ta kira sunansa a nitse. “Shettima nasanka kai kam I know baraka yi shunning Ummimi ba dan Allah ka mata magana kama mahaifiyarka magana” kai kawai ya girgiza sannan shima ya koma d’akinsa. Wajenta Fannah ta nufa tana bubbuga bayanta tana bata hak’uri tana me tabbatar mata da cewa evrything will be okay. **** A d’akin Abuu. Zaune yake a bakin gado ya had’a uwa uba tagumi yayi shiru ko kad’an yakasa comprehending abinda ke faruwa gani yake wane a mafarki wai Aysha ce ta dawo matar da har a ayau yakasa son wata mace bayan ita, matar da har a yau yakasa maye gurbin ta da wata, Aysha his first and last love, toh me tazo yi? Ina mijinta dakuma ‘ya‘yanta? shekara goma shabiyar dole ace ta haihu. “Ya Ibraheem bekamata ba kace ta fita maka daga gida nasan yadda abin yake da ciwo da zafi amman hak’uri yazama dole, dole kayi hak’uri kaje kaji dame ta taho meya kawota? Dakuma me takeso” “No Nafeesa kije ki sameta kice mata ta fita min daga gida, banason sake ganin fuskarta.” “A’a Ya Ibraheem nasan you don’t mean what you said, Aysha cefah matarka daka fiso fiye da komai, cool down kaje ka sameta muji dame take tafe please.” Tana kaiwa nan ta fice zuwa d’akin Shettima inda ta samesa miqe kan gado yayi jugum se hawaye yake zubarwa. “Ahhhh namiji dakai kake wannan hawaye Shettima gaskia ka badani yanzu in Afrah taganka haka me makeso tace? Saurayinta rago ne saboda yaga mahaifiyarsa yake wannan kuka?” Tashi yayi a lokaci d’aya yayi hugging Ummie gagam yana fad’in “kece mahaifiyata Ummie, ke kika raineni ke nasani ba itaba, she gave birth to me but you played the role as my mother, ta tafi ta barmu alokacin da muke tsantsan buqatar ta kece mahaifiyata ba itaba Ummie.” Bayansa ta hau bubbugawa a hankali “shhh! is okay Shettima inhar kamar yadda kace nice mahaifiyarka inaso kamin wannan abu guda d’aya yau kaje ka zauna a parlour ka jirani, kamata yayi kabawa Ummimi chance ko explaining kanta ne tayi muji menene amfanin dawowanta kaji son?” “Noo Ummie I don’t want to banason sake ganinta, Ummimi bata sonmu bata tab’a sonmu ba ta tafi kawai.” Breaking hug d’in tayi ta riqo fuskarsa “banason suratan banza kaji ko? Man up! Haba na Afrah ba haka fa na sanka ba tashi kaje parlour kajirani kaji? Don’t say no tashi! Tashi! ina ganinka” ba gardama ya share hawayensa sannan yafice izuwa parlon inda ya tarar da Ummimi se kuka take da Fannah a agefenta ba tare da yace dasu komai ba yanemi waje ya zauna. **** “Anas ka bud’en k’ofan nan kaji koh?” Ummie tayi maganar tana buga k’ofan d’akin Anas dayasa lock ya rufesu da Amal ciki. “Amal tashi ki bud’e.” Ido yamata nufin karta tashi aiko ta maqe tayi shiru. “Anas wai baraka bud’e ba? Sa’arka ceni nace ka bud’e!” “Toh Ummie ki fad’i me kikeso inhar maganan Ummimi zaki mana save it bamuwa so.” “Anas abinda kake be dace ba ka bud’en please.” Badan yana so ba ya tashi ya bud’e tashigo. A kan gado a gefen Amal dake kusa da Anas ta zauna tare da riqo hannayen Amal cikin nata tana mirzawa a hankali. “Amal d’ita.” “Na’am Ummie.” Kafin Ummie ta sake magana Anas ya dakatar da ita “Ummie please don’t tell her karki fad’a mata komai banason wannan yazamo silan lalacewar rayuwar Amal I can’t afford it.” “Ya Anas meke faruwa ne please ku sanar dani, meneh Ummie?” “Amal sweetie kinga matan data shigon nan ko wacce Abuu yakira da Aysha?” “Eh naganta.” “Ummie please don’t” Anas yayi pleading. “Bakiga kuna kama da ita ba? Dukanku da Ya Anas naki harma da Shettima?” “Nagani Ummie wacece ita?” “Ummiminku ce.” “Ummimin mu? Meaning?” Juyo da ita Anas yayi “listen to me carefully kinji Angel?” Kai ta gyad’a. “Good kinga Ummie nan ko?” Nan ma ta gyad’a kai “who is she to you?” “My mother mana Ya Anas, she is all our mother, Ummie mamanmu ne dukan mu koba hakaba Ummie?” Shiru Ummie tayi takasa amsa Amal tsantsan tausayi yau shekarun ta goma shabiyar amman ace batasan wace asalin mahaifiyarta ba, batasan ta ina zata fara mata bayani ba. Kanta ya karkato zuwa direction nasa. “I’m sorry Amal.” abinda ta iya cewa kenan. “Ummie ba mahaifiyarmu bace Angel, ba ita ta haifemu ba she just played the role as our mother amman ba ita bace asalin mahaifiyar mu Ummie is our foster mother Ummimi wanda Abuu yakira da Aysha a while ago itace mahaifiyarmu ita ta haifemu kingane?” Hawaye tasoma zubarwa alokaci d’aya sam k’wak’walwarta yakasa comprehending abinda ke faruwa kamar ya Ummie ba mahaifiyar ta bace. “Ya Anas bangane ba, bangane me kake nufi ba? Taya zakace Ummie ba mahaifiyata bace, ba mahaifiyarmu bace duka? Taya zakace wancan matan datazo wanda ban tab’a ganinta ba se yau itace mahaifiyata? Why Ya Anas?” Hannu yasa ya share mata hawayen. “Angel banason ganinki kina kuka.” “Then tell me you are not telling the truth” cike da tashin hankali ta juyo tayi hugging Ummie. “Ummie you are my real mother right? Kece mahaifiyata bawata daban ba Ummie you are my mother please say yes, Ya Anas be gane bane you are my mother and no one else” itama Ummien kuka take sosai na sosai da k’yar ta d’aga Amal daga jikinta tasa hannu ta share mata hawayen. “Amal I’m so sorry kinji? Ban tab’a sanar dake gaskiya ba, na tauye miki hak’k’inki na sanin asalin mahaifiyarki amman kisani nayi hakan ne for your sake, wanki Anas ne yahana a fad’a miki gaskia sabida yadda yakeson ki bayanson abinda ze lalata miki rayuwa, bani bace mahaifiyarki Amal Ummimi ce ta haifeki itace mamanki na asali.” “Noo Ummie ni kece mahaifiyata and no one else kece ba ita ba she is a bad person banasonta ban santaba.” Ta rushe da kuka, hugging nata Anas yayi yana bubbuga bayanta har seda tayi shiru. “Ya Anas inhar ba Ummie ce mahaifiyata ba then wacece ita? Mesa take zama damu kullum?” “Ummie sister’n Abuu ne bakiji Abuu na kiranta Nafeesa ba? Asalin sunanta kenan but ana cemata Ummie shiyasa time da ta dawo zama damu tun kafin a haifeki muke kiranta Ummie, dalilin daya sa ta dawo zama damu kuwa shine sanadin barin mu da Ummimi tayi” “Toh in haka ne mesa ban tab’a sanin Ummimi ce mahaifiyata ba? Inhar dagaske kai da Ummie kuke wancan matar itace mamanmu mesa bata zaune damu?” “Kinason kisan dalilin Angel?” Ta gyad’a mai kai. “Saboda batada imani Angel, bata da tausayi bata sonmu.” “Anas don’t talk about your mother like that” Ummie ta katsesa “uwa uwa ce komin rashin dad’inta.” “No Ummie kibari in sanar da ita dukkannin abinda Ummimi tayi mana sabida kar ta tausaya mata.” “Anas I said no.” “I’m sorry Ummie amman ya kamata Amal tasan abinda mahaifiyarta ta mata” nan ya cigaba “Amal Ummimi bata tab’a sonmu ba zaki iya tuna ciwon dake a hannu na wanda nace miki agarin ball aka jimin?” Nanma ta gyad’a kai. “Its a lie kinga matar dake parlourn, Ummimi ita tajimin ciwon, she left us for another man 15 years ago...” nan ya kwashe labarin komai yabata ba tare da yabar komi a baya ba. Kuka sosai Amal take Ummie takwantar da ita a jikinta. “Ummie mena mata? Mesa ta tsaneni? Mesa bata bari naji d’uminta ba?” “Shhh! is okay sweetheart ya isa kinji? Bar kukan haka, duk abinda ta miki she is still your mother-” katseta Amal tayi tare da d’agowa daga jikinta “No Ummie you are wrong Ummimi ba mahaifiyata bace, ita ta haifeni amman ke nasani as mahaifiyata saboda haka you are my mother right Ya Anas?” “Yes Angel come here” nan ta matso jikinsa yayi hugging nata “is okay bar kuka kinji?” “Ya Anas promise me Ummimi batazo dan tafiya dani bae, bana sonta kamar yadda tak’i ni tun ina baby, Ya Anas karka barta ta tafi dani please.” “That will never happen Angel.” “Anas ya isa please be kamata kasawa Amal tsanan mahaifiyar ta haka ba koda meh Ummimi tayi she is still your mother yanzu ku tashi muje mu sameta a parlour banason jin no ku tashi.” **** A parlour. “Shettima, Shettima d’ana dan Allah kamin magana I’m sorry for what I did to you dan Allah kayi hak’uri.” Anan ta miqe ta nufo inda yake zaune ta dafe kafad’ansa, hannunsa yasa yacire nata shima yana hawaye “Shettima please kayi hak’uri.” “Ummimi why? Mesa zaki dawo bayan mun mance dake? Why do you have to mess up our lives always? Why Ummimi?” Ya rushe da kuka tsugunawa tayi gabansa tare da hugging nasa sam be hanata ba sede beyi hugging nata back ba, yana kuka tanayi Fannah na kallonsu sun kusan minti biyu a haka sannan ya raba jikinsa daga nata. “Shettima wallahi ba’a son raina na tafi na barku ba I love you guys so much” ta yi maganan hannunta dafe akan fuskarsa tana shafawa a hankali. “Sharrin shaid’an ne ba komai ba Shettima dan Allah don’t stop me from being a mother to you kabani dama in biya wannan shekaru goma shabiyar da mukayi ba’a tare ba please this is all I ask nasan barin iya tambayan gafarar ka ba saboda ban cancanci hakan ba ni kawai kabani dama in zame maka mahaifiya again please Shettima.” Shiru yayi bece komai ba. “Shettima kayi shiru” Fannah tayi maganar tana d’ago Ummimi daga k’asa. Daidai nan Abuu yafito idanunsa sun mugun kad’awa bayanshi Ummie ne da Amal sekuma Anas. Bayan sun zazzauna Abuu yayi gyaran murya; “Aysha meke tafe dake? Me kika zo yimin a gida? Ko ban tambaya ba nasan sharri ne tattare dake saboda haka in kinayi wa Allah kitashi kifita min daga gida, nida yarana bamu k’aunan ganinki, bak’in cikin da kika bamu da abaya kad’ai ya ishemu basekin k’ara mana.” “Ya Ibraheem please ya isa kayi hak’uri” cewar Ummie. “Amal taho nan” Abuu yakirata seda ta kalli Anas yabata nod tukuna taje tasamu Abuu, a gefe dashi ya zaunar da ita. “Zaki iya tuna wannan?” Ya tambayi Ummimi da tuni kuka yafi k’arfinta. “Zaki iya tuna ‘yar da kika k’yamata kika turo ta kamar shegiyar da batada uba acikin basket? Zaki iya tunawa?” Har k’asa ta sauqa kan guiwanta tana roqan Abuu. “Ya Ibraheem dan darajan ubangiji kayi hak’uri, kayi hak’uri dan Allah wallahi baroku danayi shine babban kuskuren dana tafka a rayuwa na, d’an Adam ajizi ne we all make mistakes nasani kuskuren danayi babba ne wanda se me imani da tausayi ze iya yafemin, Ya Ibraheem wallahi nayi nadaman abinda na muku musamman ma abinda nayi ma Amal.” Nan ta dawo da kallonta kan Amal. “Amal dan Allah kiyi hak’uri kiyafewa mahaifiyarki I’m so sorry Amal please forgive me, give me the chance to hold you in my arms Amal tunda na haifeki ko k’are miki kallo banba nasa aka nad’eki cikin tsumma aka turoki ban tab’a riqeki ba Amal wannan abu har a yau yana damuna barin tab’a samin sukuni ba a rayuwa na har se in na riqeki as mothers do dan Allah karki hanani please my Amal.” Hannu Amal tasa ta share hawayenta sannan ta miyar da kallonta kan Abuu. “Abuu mena tab’a mata ta tsaneni haka? Mesa baka tab’a fad’amin inada wata mahaifiya ba bayan Ummie? ” “Amal kiyi hak’uri kinji? Nasan mun miki laifi wanda yake babba na hanaki sanin asalin ki, kisani nayi hakan ne saboda ina sonki Amal banason ki tashi kina kewar mahaifiyarki, I’m sorry kinji? Bar kuka” yasa hannu ya share mata hawaye. “Angel zo abinki” Anas ya kirata ba gardama taje ta samesa. “Abuu nida Angel zamu d’an fita in kun gama abinda kukeyi call me se in d’au Fannah.” “Anas dan Allah karka tafi kabari in nemi gafarar Amal please.” “Amal zaki iya yafe mata tauye miki hak’k’in datayi? Zaki iya yafe mata wulak’antaki da tayi since you were a baby?” Kafin Amal ta amsa yacigaba “no that the answer daga ni har Amal bame yafe miki sede ko Abuu da Shettima kina iya hak’uri in maganganun dana fad’a miki are a bit harsh to your ears, hakan na nuni da tsantsan tsanan da nake miki ne Ummimi dukda cewa kina mahaifiyata.” “Anas enough!” Ummie ta daka masa tsawa “kai bakasan wannan mahaifiyarka bace kake gasa mata bak’k’en kalamu haka iya son ranka? Ya Ibraheem kamishi fad’a.” “Anas yayi laifi Nafeesa, amman kuma in kika lura Aysha itace sila da ace bata aikata abinda tayi 15 years back ba da Anas bare tab’a gaya mata munanan kalamu haka ba, I’m not saying Anas is right what am saying is he has a point mukad’ai muka san kalan hell da mukayi witnessing da wannan marar imanin ta tafi ta barmu. Aysha me muka tab’a miki? Talaucin da kika tafi kika barmu danshi kisani bamu muka d’aura wa kanmu ba, gashi nan kinzo kin gani da idanunki Allah ya yaye mana shi saboda haka me kika zo min a gida?” “Tabbas ba k’arya ko kuskure a magananka Ya Ibraheem Allah shike azritawa aduk sanda yaga dama, inda zan iya bayyana muku how sorry I am da nayi, inda kunsan kalan tashin hankalin dana shiga bayan barinku danayi, wallahi tun a duniya anan naga sakayyan butulcin dana muku shiyasa nake barar gafararku Ya Ibraheem inhar baku yafemin ba bansan a’ina zan sa kaina ba bansan ya zaman kabari ze zame min ba ku agaza please. Ya Ibraheem inhar kai baka yafemin ba ba yadda yaran nan zasu yafemin please ka taimaka, Ummie dan Allah kisa baki ko zejeki.” “Ya Ibraheem kayi magana please godiya yakamata muyi tunda har Aysha tagano kuskurenta kuma tayi repenting se ku kuma kuyi hak’uri ku tausaya ku yafe mata, Aysha ko zaki bamu labarin ya rayuwarki ta kasance cikin wannan shekaru goma shabiyar dasuka shud’e ba tare da kowa yaji ko ya ganki ba? Ko ban tambaya ba nasan kina cikin babban tashin hankali jikinki kad’ai amsa ce game tambaya in shaa Allah, in family’nki sukaji labarinki zuqatansu zasu kariya su yafe miki.” “Nagode Ummie” tayi maganan tare da komawa kan kujera ta zauna. “LABARI NA bashida dad’in sauraro, ba komai bane aciki banda k’uncin rayuwa wanda ni dakaina na d’aura wa kaina saboda kwad’ayin kayan duniya dana sa a gaba, kwad’ayi ya kasance halin mata dayawa a rayuwarmu na yau. A gaskia duk wacce tad’au kwad’ayi abinyi toh wallahi tana tattare da gwagwarmayar rayuwa saboda kwad’ayi ba abar yi bace. Labari na wanda yasamu asali tun daga ranan dana bar gidan Ya Ibraheem nabi Alhajin Yola shine mafi mumunan labarin da na jima banji ban kuma gani a real life ba sede a labarai.” Taja numfashi sannan ta cigaba... *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [13:00, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💞* 9⃣5⃣ _“A yinin ranan da nabar gidan Ya Ibraheem nabar yarana abin muradina Anas da Shettima badan komai ba sedan bak’in talaucin daya addabemu sau dayawa muna tashi ba abinchi bayan gashi a waje Alhajin Yola ya nuna yana sona yana kashe min kud’i ba tare da na kawo wani tunani a raina ba na tattara kayakina nabar gidan Ya Ibraheem dukda erin kuka da roqana dasu Anas suka rik’ayi hakan be hanani tafiya ba saboda alokacin kwad’ayi ya riga ya rufemin ido”._ _“Bayan nabi Alhajin Yola yawuce danu Yola a ranan inda muka sauk’a awani had’ad’d’en hotel, seperate d’aki yakama mana acewarsa bamuyi aure ba tukuna be dace mu had’a d’aki ba washegari ya tinkareni ya fad’amin abinda ke zuciyarsa na aurena dayakeson yi dukda nasan haramun ne aure akan aure hakan be hanani amincewa da k’udirinsa ba, achan Yola aka d’aura mana aure acikin sati yamana processing visa inda muka wuce tsarkacacciyar k’asa Saudi yin honey moon sede wani gudu ba hanzari ba tun isar mu chan nake fama da zazzab’i, zuwan mu asibiti aka tabbatar mana juna biyu ne d’auke dani cikin Amal kenan, barin b’oye muku amman a lokacin cewa ma nayi azubar da cikin kasancewar chan gari ne me tsarki basu aikata haramun aka k’i biya min buk’ata koda muka dawo gida hankalina a tashe yake tsoro na kar Alhajin Yola yace ya fasa zama dani tunda na taho masa da cikin wani gidansa, alokacin banida wata burin data fi in kasance dashi saboda yadda yake kashe min kud’i. Shi ya kwantar min da hankali yakuma tabbatar min da cewa in kwantar da hankalina inyi rainon cikin kar na zubar yaso in na haife se na dawo muku da abunku, without a second thought na amince da hakan, haka nata rainon cikin Amal daya bani wuya har fiye da na Anas cikin fari dalilin haka yasa natsani abinda ke cikin ko ante-natal d’ina ba regularly nake zuwa ba fata na Allah rabani da abinda ke cikin nawa lafiya.”_ _“Munyi tsawon watanni 7 a Saudi ba tare da mun samu sab’ani da Alhajlin Yola ba tarerayata yake kamar ‘yar baby abinda nakeso shi yakemin alokaci d’aya na mulmule tunda nafita daga first trimester. A wannan watan ne muka dawo Nigeria inda muka sauk’a a Maiduguri nacigaba da rainon cikina dana tsanesa fiye da mutuwa, kwatsam da daren wata rana nak’uda ya taho min wanda nad’au mutuwa zanyi bayan kusan awa shida danayi a labour room nasamu Amal ko k’are mata kallo banyi ba, in tambayi nurse d’in mace ce ko na miji ma banba saboda jin dad’in da nake na rabani da ita ko shi da Allah yayi, naso barin ta ta kwana a asibiti amman sunka k’i dole na taho da ita gida anan ne na gano mace ce na haifa duk erin kukan da Amal take a lokacin dan yunwa besa na shayar da ita ba yaron dake mana d’an hidima ne yabata ruwa ta rik’a sha kafin garin Allah ya waye Alhajin Yola yasa sa a mota da Amal tare da letter dana rubuta aka kawo muku ita”._ d’ago kai tayi ta kalli Amal dake ta kuka jikin Anas kamar ba gobe taji ta k’ara tsanan kanta na wulaqanta wannan kyauta da Allah yayi mata. _“Se a wannan lokaci nakai Alhajin Yola gun iyayena basu ko damu taya nayi auren ba tambayar da suka min d’aya ne shin yanada kud’i? siyayyan da Alhajin Yola ya musu ne yazame masu amsa, k’arya namusu nace ka saken ne Ya Ibraheem shiyasa na sake aure, please kayi hak’uri ka yafemin na sharrin dana maka”..._ “Ko kad’an baki min sharri ba Aysha saboda aranan da kikayi stepping foot kika bar gidana a ranan na miki saki d’aya saboda nasan duk inda zakije aure zakiyi nikuma ina sonki barin iya jure fushin Allah akanki ba shiyasa na sauwak’e miki kinga ko bakiyi aure akan aure ba.” wani sabon kukan ya sake rufe Ummimi she can’t ever forgive herself. “Tabbas babu kaman ka acikin mazaje Ya Ibraheem nagode k’warai Allah yima sakayya. _“Daga nan muka wuce New York kamar yadda yamin alk’awari, rayuwa bata tab’amin dad’i kamar a wannan lokaci ba sede abin mamaki koda na tambayi Alhajin Yola wani aiki yake seyace min he is self employed niko da dama kud’insa ne ya damen ban kawo wani abu a raina ba haka muka d’au tsawon shekara muna soyayya dashi ba tare da mun samu wani matsala ba iyayena kuwa kullum yana cikin musu alkhairi daban daban a shekara na biyu da aurenmu ne nasamu cikin Barrah da Basmah wanda suka kasance twins kyawawa wane Amal shekarunsu uku nasamu Yusuf wanda yake sak Anas shi kuma, harta blue eyes nasu iri d’aya”_ ta d’ago kai tana kallon Anas da take ya kawar da kallonsa daga gareta, hawayen ta ta share sannan ta cigaba; _“Alhajin Yola ya kasance yana matuqar son ‘ya‘yansa becika tsawata masu ba koda sunyi laifi ne, haka rayuwa ta cigaba da kasance mana cikin jin dad’i alokaci kad’an ne nake tunawa dasu Anas da Shettima amman kuwa in na tuna da talaucin daya fitini gidan Ya Ibraheem sema inji na tsanesu tun daga kan Yusuf haihuwa ya tsaya min. Su Barrah suna da 12 years aduniya nasoma fuskantan chanji daga mahaifinsu mutumin da baida magana baida masifa yamiyar da masifa abinyi abu kad’an kayi seya tsigale ka, akwai lokacinda har mari na yayi saboda yana ma Yusuf fad’a nashiga toh tun daga wannan lokaci ban sake gane kan mahaifinsu ba, yadena sonmu kullum cikin k’untata mana yake school fees na makaranta ma seya ga dama yake biya musu nayi nayi ya gayamin inhar laifi na masa ya fad’a mani in basa hak’uri amman ina inya watsa min wani mugun kallo ni dakaina nake tashi masa agun a 13th birthday’n su Barrah yayi suprising namu duka, birthday cakes biyu ya siyo musu mukayi celebrating birthday nasu washegari yasa duka yaran cikin mota cewa ze kaisu park su shaqata yatambayeni ko zani nace mai a’a bansani ba ashe wannan rana shine rana na k’arshe da zan sake sa yara na a idanu na ba_. Kuka ne yafi k’arfinta hankalin kowa ya tashi wajen banda Anas, duk sun k’osa suji meya faru, Ummie da Fannah ne ke bata hak’uri. Picture’n taciro ta miqa ma Ummie “yau watanni bakwai kenan da rasuwansu.” Salati kukeji a d’akin bayan Ummie tagani ta miqa wa Abuu se Shettima lastly Amal then back to Ummimi again, anan duk sukayi mata ta’aziya shima Anas badan yanaso ba yayi mata. _“Tun safe ya fita min da yara har La’asr basu dawo ba kodana kira wayansa kuwa har ta tsinke be d’aga ba wayoyin su Barrah kuwa switched off yake cemin, anan fa hankalina ya tashi daman tun tafiyarsu nake ji ajikina something bad will happen to them nakasa zama gu d’aya fatana Allah dawo min dasu lafiya se bayan Isha’i naji k’aran bud’ewan gate a guje na fita waje bayan yayi parking na tsaya gun ina jiran fitowan farin cikina yara na, sede basu ba alamansu, mahaifinsu kad’ai nagani cike da tashin hankali na tambayesa ina yaran suke kallo na yayi a raunane sannan yace min wai an sacesu, bansan a lokacin dana sume wajen ba next abinda nasani shine gani na danayi kwance akan gadon asibiti se a washegari muka dawo gida ba kalan tambayan duniyan da banma Alhaji Isma’il ba ya fad’amin ina ‘ya‘yana, amsar nasa d’aya ne an sacesu jiya a park cike da tashin hankali na d’ago mayafina zan kai report station ganin haka munafikin ya dakatar dani yamin qaryan wai tun jiya yakai report yanzu haka police sunakan investigation haka har wani sati ya zagayo ba labarin yarana, ban sake sanin meke min dad’i ba akullum ina sa ran za’a samu su Barrah amman inaa adaren wata rana na fito daga d’akina zan wuce dining space dan shan ruwa naji Alhaji Isma’il akan waya har na wuce se wani abu ya dawo dani baya nakasa kunne ina sauraron meyake fad’i a wayan. Hankalina ya matuqar tashi jin da bakinsa yake fad’in “ran yara na uku dana baku be isheku ba yanzu na mata ta kukeso?” Innalillahi wa’ina ilaihi raji’un”_ _“Mutuwan tsaye nayi a wajen totally speechless ban hankara ba naga Alhaji tsaye a gabana fuska nakad’ai ya zame masa amsa ga tambayan daya s min. Ina kuka na mai maganar, “Alhaji? Dagaske ne?” Na tambayesa. Kame kame yasoma bansan a lokacin dana fara kai masa bugi ba, ba kalan zagin da ban masa ba a daren nace zan kai k’aransa station nan ya kukkule duka k’ofofin gidan da dambe da fad’a yakaini wani d’aki ya rufeni, ina jinsa yayi waya da d’aya daga cikin ‘yan k’ungiyan nasu yana cemai ya yarda ze sihar dani nima acewarsa tunda nasan sirrinsa yanzu ba amfani na again, ba waya akusani dani koda akwai ma bansan wa zan kira ba kwana nayi ina Sallah Allah ya kub’utar dani daga sharrin sa, washegari nasome neman abinda ze taimaka min in b’alla lock na k’ofan, da cokalin da nasamu na b’ab’alle screws d’in k’ofan na fito a lokacin bayi gida yafita, kayaki kad’an na d’auko da sauran essential things da zan buk’ata, na nemi wayana sama da k’asa na rasa, a gurguje nabar gidan nakai report police station ko ya akayi maganan yaje kunnensa oho next abinda naji shine wai yagudu yabar k’asan kwata kwata tun daga wannan rana ban sake sa shi a idanu na ba 3 months ago na ganshi awani super market tundaga wannan lokaci na shiga b’uya saboda nasan aduk lokacin da ya ganni tabbas nima siyar danayi zeyi, aiki na samu awani restaurant as a cleaner dashi na dogara har izuwa lokacin dana had’u da Anas da Fannah, kunji takaicaccen labari na.”_ Tausayinta ne yakama kowa a d’akin harta Anas, seda Ummie ta zubar da hawaye. “A gaskia kinsha gwagwarmaya a rayuwanki Aysha ba abinda zamuce se Allah ya kare aukuwan na gaba ya tsaremu daga sharrin mutane da aljanu gabad’aya...” dadda’d’un kalamu Ummie tariga gaya wa Ummimi shi kansa Abuu ya mugun tausaya mata yasani alhak’in sune yakama ta tunda har a duniya taga sakayya yaci ace sun yafe mata suma. “Aysha ni na yafe miki na yafe miki har abada abinda ya faru dake kuma Allah takaita” cewar Abuu. “Ya Ibraheem nagode, Allah ya saka da alkhairi, Shettima, Shettima dan Allah ka yafemin abinda na maka.” Shiru yayi bece komai ba ba irin rok’an da bata mai ba seya bud’e baki zece ya yafe mata seya kasa haka ta dawo kan Amal ma duk ba wanda ya iya ya yafe mata Anas kam ba magana Abuu be sa baki ba saboda yasan ba’a shiga tsakanin uwa da yara yasani with time duk zasu yafe mata. *** Abuu ne tsaye da Ummie a dining ayayinda Ummimi ke zaune da Fannah a parlour su kad’ai Anas da qannensa duka sunyi d’aki. “Ya Ibraheem yanzu ya zakayi da Aysha?” “Ni kaina bansani ba Nafeesa, bansan me zanyi da ita ba.” “Agani na mubarta ta zauna damu anan tunda ba inda zata iya zuwa batada kowa banda mu.” “Me kike nufi Nafeesa?” “Ina nufin ka dawo da ita d’akinta ai akwai aure a tsakaninku.” “Barin iya dawowa da Aysha ba ina sonta amman barin iya dawo da ita ba.” “Zaka iya Ya Ibraheem kayi hak’uri mukoma parlon.” Bayan sun dawo suka zauna Ummie tayi gyaran murya “Aysha kinje kinga iyayenki kuwa?” “Banje ba tukuna bansani ko iyayen nawa ma suna raye ba.” “Kinada masauk’i yanzu?” “Banida Nafeesa.” “Toh yanzu wani mataki kika d’aukar?” “Ba abinda nakeso kaman in kasance da ‘ya‘yana Ya Ibraheem dan Allah kayi hak’uri ka dawo dani d’aki na badan halina ba dan Allah.” “Aysha na soki kuma zan cigaba da sonki amman ban tsammanin zan iya dawo dake.” “Ya Ibraheem please karka min haka dan Allah karka hanani daman kasancewa da yarana again nayi kuskure amman wallahi na tuba barin sake aikata abinda nayi da a baya ba, ka taimaka please” “Aysha kiyi hak’uri amman barin iya dawo dake ba” yana kaiwa nan ya miqe. Hak’uri sosai su Fannah suka rik’a bata. Da k’yar Ummie ta samu tayi convincing Abuu ya yarda aka bawa Ummimi d’aki d’aya a gidan Anas najin haka yasa Amal ta had’a akwatinta suka koma gida tare yasan muddin Amal tacigaba da zama da Ummimi toh eventually Amal zata yafe mata abinda baiso kenan. **** Tun isar su Fannah gida bata ma Anas magana ba a d’akinta Amal ta sauqa daidai da Azahar Anas yatura Amal dataje ta kira Fannah suyi Sallah a d’akin Hanan ta tarar da ita bayan tayi sallama tace, “Ya Fannah wai kifio muyi Sallah inji Ya Anas.” “Kice masa yajaku ku biyu zanyi nawa da kaina” da “toh” Amal taje ta isar wa Anas da saqon Fannah, daman yau yasan da akwai drama shida kansa ya miqe yaje yasamu Fannar, agefenta ya zauna “Flower tashi muje muyi Sallah.” “Bakaji meh Amal tace maka bane? Nace kajaku zanyi nawa ni kad’ai.” “Mesa toh?” kafin yakai hannunsa kan cikinta taja da baya. “Mara na namin ciwo se anjima zanyi.” “Toh zamu jiraki.” “Ni ina ma ace yadda kakemin haka kake ma Ummimi wallahi Habeebi ko kad’an banji dad’in abinda kama Ummimi ba yau, uwa uwa ce fa you are not being just inhar kai baraka yafe mata ba then don’t drag Amal into it, I know ba tsakani da Allah kasa Amal had’a akwati ta biyomu ba gudun kar ka barta achan eventually tayi forgiving Ummimi ne koba haka ba?” “Ke kikaji wajen zaki tashi muyi Sallah ne kokuwa?” “Bansani ba nima” tana kaiwa nan tabar masa d’akin binta yayi da kallo yana cizen lips nasa, d’akinsa takoma haka tak’i binsu Sallah ita kad’anta tayi nata bayan nan suka soma jin yunwa sarai zata iya musu girki tace barata iya ba Amal ‘yar gata kam dama ba abinda ta iya yi koda Anas yace ze musu girkin Fannah ta b’ullo da dabara tace ita yau tuwo takeson chi tasan sarai ba iyawa yayi ba. “Flower tuwo kuma yau?” “Eh tuwo nakeso.” “Toh Mom Hanan Amal jeki d’au mayafinki muje musiyo mata.” “A’a Amal is staying with me akwai aikin danakeson ta tayani bayan tafiyan mu cleaners d’in ba kullum suke zuwa aiki ba d’akina duk yayi k’ura zamuyi dusting.” “Flower bakida lafiya kibari gobe sukazo se suyi.” “Don’t worry ai bawani aiki bane zaki tayani koh Amal?” “Why not Ya Fannah.” “Good muna jiranka kefa barakichi tuwon ba asiyo dake?” “A’a banachi banaso.” “Ya muku kyau keda wannan yayan naki wato bakiya chin tuwo kema? Seku nemi abinda zakuchi nide aje asiyo min tuwo da miyan yakuwa I’m hungry.” “Toh Mom Hanan” yayi maganan tare da rufe gab dake tsakaninsu daidai zeyi pecking goshinta kenan taja baya sakamakon haka Amal ta k’yalk’yale da dariya “wai! Wai! Su Ya Anas ansha boncy, an kwashi shoki” itama Fannar bata san lokacinda ta qyalqyale da dariya ba. “Wato ni kikayi shunning a idan Amal ko Flower?” “Ni kaje ka siyo min abinci abeg yunwa nakeji.” “Kin kyauta kekuma Amal ina dariya kikemin nafasa bada iphone 7 d’in ma Shettima zan bada.” “A’a Ya Anas please I’m sorry”*** Bayan tafiyan Anas Amal ta d’auko bucket da towel dan fara goge-gogen da Fannah tace zasuyi sede ta tarar da Fannah zaune a parlour. “Ya Fannah kince akwai goge-gogen da zamuyi.” “Wasa nake babu zo nan ki zauna” tayi mata nuni da space dake gefenta “zamuyi wata magana” ba gardama taje ta zauna. “Amal ke ba yarinya bace yanzu you are 15 years old kinsan whats right and wrong koba haka ba?” Ta gyad’a kai “good” Fannah ta cigaba “inason ki saurari abinda nakeson fad’a miki da kunnen masu hankali ki ajiye duk wani abinda Ya Anas naki ya fad’a miki a gefe do you get me?” “Yes Ya Fannah.” “Mesa kika k’i ma Ummimi magana? Baki tausaya mata ne she lost 3 of her children, three fa Amal how does it feels ke lokacin da classmate naki nema yarasu ya kikaji balle ace ‘yan daka haifa har guda uku kana ji kana gani aka siyar dasu, just how bad does that feels?” shiru Amal tayi bata iya tace komai ba. “Magana nake miki Amal.” “It feels bad.” “Good then meya kamata kiyi dan sata feeling better kuma?” “Inyi condoling nata in bata hak’uri.” “Exactly amman mesa bakiyi ba?” “Ya Fannah ni kin manta abinda tamin ne danake baby? She hated me batare dana mata komai ba ko shayar dani batayi ba, to cut the crap har cewa tayi zata zubar da cikina kuma ga ciwon dataji ma Ya Anas nifa bana sonta.” “Kai kai ya isa haka ya isa karki sake fad’in bakiya son Ummimi, kema Anas ya koya miki wannan banzan halin nasa ko? Ya cusa maki tsanan mahaifiyarki, waya gaya miki ana k’in uwa ne?” “Ya Fannah nifa ba k’inta nayi ba ita ta k’ini, ita mesa baraki mata magana ba.” “Ai na mata Amal we humans we are prone to make mistakes ko ke nan akwai mistakes da kikayi kuma akwai dayawan da zakiyi a gaba haka Allah ya hallice mu we aiint perfect amman kuma the best amongst us shine wanda yayi laifi yayi realising yakuma tuba kamar yadda Ummimi tayi kiga kukan data tayi mana d’azu akan yaran data haifa kinsan da zata bud’e baki ayau tace ta tsine muku gabad’aya bameyin albarka cikin ku kin sani?” Amal ta kad’a kai. “Kinga shiyasa, Amal duk abinda zakiyi ma Ummimi aduniyan inma duniya zaki siya mata wallahi barekai kwatankwacin d’aukan cikin ki datayi ta reneshi har ta haifeki ba, kinsan azaban haihuwa kuwa? Ba zafin daya fishi se mutuwa fah shiyasa akace duk wacce ta mutu ta hanyan mutuwa ‘yar aljanna ce tayi mutuwan shahada, uwa uwa ce komin rashin dad’inta koda cikin shege tayi ta haifeku wallahi shima abu ne our mothers are priceless ba abinda zamu iya musu in return of abinda suka mana.” *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [13:00, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💞* 9⃣6⃣ “Toh ni yanzu me kikeso in mata Ya Fannah?” “Kema ai kinsani Amal kidena biyewa Ya Anas kibata chance da take nema to hold you and be your mother bawai nace kiyafe mata bane amman kibata wannan chance da takeso dakanki zaki yafe mata in kikaji dad’inta ke bakison kisan mamanki ne?” “Ai nasan Ummie.” “Ummie ba itace mahaifiyarki ba Ummimi ce mahaifiyarki...” haka Fannah tariga ma Amal nasiha seda ta kashe mata jiki. Dawowan Anas ya taho ma Fannah da tuwonta nan tasamu ta kora yunwa shikuma da Amal suka wuce kitchen dan dafa nasu kamar Anas yasani ya tambayi Amal ko Fannah tamata maganan Ummimi bayan fitansa, bata b’oye masa ba ta fad’a masa zahirin gaskia. “Ya Anas don’t you think is about time mu bawa Ummimi chance to be our mother? Wallahi wa’azin da Ya Fannah tamin ya mugun tsorata ni.” “Ai dama nasani, nasan hakan ze faru kinaji na ba bawani chance da zakibawa Ummimi am I clear?” Baki na rawa tace “yy.. Yes.” _Washegari..._ Da sassafe Ummimi ta tashi tayi wanka sannan ta rok’i Ummie data rakata kitchen dan nuna mata inda postions na plates da sauran utensils suke hakan kuwa akayi breakfast me rai da lafiya favorite na Abuu ta had’a wato doya me k’wai a jiki bayan tagama ta had’a kan dining. 8:30AM Abuu yafito daga d’akinsa cike da ladabi da biyayya ta sauk’a har k’asa ta gaishesa ba yabo ba fallasa ya amsa. “Ya Ibraheem ga breakfast chan na had’a maka dan Allah kar kace bara kaci ba kayi hak’uri please” kai ya gyad’a mata sannan yabita dining d’in taja masa kujera ya zauna sannan tasoma serving nasa tana bud’e flask d’in k’amshin girkinta wanda he can’t tell how he missed it ya buga masa hanci bayan tayi serving nasa ta had’a masa tea sannan ta koma gefe tana kallonsa a hankali yasoma chin abincin har ya k’are. “In k’ara maka ne?” Ya gyad’a mata kai dad’i sosai taji a ranta “ashe har a yanzu baka dena son doya me k’wai ba.” “Mesa zan dena so bayan kin riga kin saba min dashi, kefa barakiyi breakfast d’inba?” “Zanyi amman nafison duk ku karya tukuna, Shettima fah? Har yanzu yana kai goman safe kafin ya tashi kokuwa ya rage bacci?” “Keda d’anki kuma kina iya zuwa kiduba d’akin sa ai shine first room by your right.” “Toh nagode sosai Ya Ibraheem.” Seda yagama chi ta masa Allah kare ya fice office sannan ta dawo ta d’iba wa Shettima nasa a plate da tea nasa ta nufa d’akinsa a hankali tayi knocking. “Waye ne” ya tambaya. Da k’yar bakinta ya iya cewa “Ummimi ce Shettima.” Daga nan be sake cewa komai ba. “Shettima yi hak’uri ka bud’en kaji? Yi hak’uri please.” Nanma shiru “Shettima barin bar nan ba har se in ka bud’en k’ofan nan.” Tafi minti goma tsaye a wajen sannan Shettima ya tashi ya bud’e mata ba tare da yace mata komai ba, bayansa tabi ta ajiye masa breakfast d’in akan centre table dake d’akin. “Ina kwana Shettima?” Nanma be amsata ba gefensa ta nufa ta zauna kan gado. “Shettima barin iya forcing naka kayimin magana ba saboda na kasance me laifi amman kayi hak’uri ka tashi ka karya kaji Babana?” “Ummimi why are you doing this?” “Saboda inason ka Shettima, ina sonka fiye da yadda nakeson kaina.” “Shine kika tafi kika barmu alokacin da muke buk’atanki?” “Barin ku danayi shine babban kuskuren dana tafka kuwa Baba na shiyasa nakeson inyi making up for the last 15years da mukayi ba a tare ba, yi hak’uri ka karya kaji?” Hannunsa taja ta zaunar dashi sannan da kansa ta soma basa abincin yana karb’a har yagama chi. “Thank you so much Shettima na wannan dama da kabani Allah ya saka maka da alheri yakuma maka albarka.” “Ameen” ya amsa. Daidai nan wayarsa yasoma ringing kasancewar wayar na kusa da Ummimi tasamu daman ganin wake kira ‘honey boo’ taga rubuce kan screen d’in. Da sauri ya d’aga wayar daga dubanta sede yakasa amsawa ganin Afrah ke kira, d’an murmushi ta saki “haka Baban nawa ya girma? D’aga wayar mana to ko se surikar tawa tayi zuciya ne?” Besan alokacinda ya murmusa ba. “Ko kunyan Ummiminsa yake ne?” “Ummimi fa ba budurwa ta bace.” “Awww shine akayi saving lambarta da honey boo, d’aga mana kose ya tsinke ne.” “Zan kirata anjima.” “Toh wace ita? Wata lucky girl d’in ne ta sace min zuciyan one in town son d’ina?” Murmushi sosai Shettima ke “sunanta Afrah k’anwar Fannah.” “Wow aiko ina da tabbacin itama tana da hankali kamar Fannah, Allah tabbatar mana da alkhairi yabar ku tare.” “Ameen Ummimi” “I will love to know you better Shettima” “Don’t worry” yayi maganar yanasa shirt nasa. “Toh Babana ya naga kamar kana shirin fita?” “Eh makaranta zani inada lectures.” “Oh okay me kakeso kaci da rana?” “Babu ba sekin dafamin komai ba zan siya a school.” “A’a mahaifiyarka na raye bara ka chi abincin waje ba fad’a min meh kakeso.” “Ina irin macronin da kike dafa mana? Irinshi nakeso.” “Toh angama son Allah kiyaye kaji? I love you.” So yake yace mata he loves her too amman kuma yakasa dan haka ya gyad’a mata kai zallah. Bayan tafiyan Shettima ta share masa d’aki tayi mopping tsatsaf haka d’akin Abuu ma sannan tasake yin sabon breakfast masu Anas tare da Ummie suka fita dankai musu sede Ummie tak’i shiga tabar Ummimi ita kad’ai, securities suna ganin Ummie suka bar Ummimi tashiga door bell ta danna alokacin Anas na aka kitchen shida Amal suna had’a musu breakfast ita ya tura da taje ta bud’e ganin Ummimi ce ta bud’e tare da gaisheta kamar yadda Fannah ta buk’ace ta. Dad’i sosai Ummimi taji “Amal my princess ya kike?” “Lafiya.” “In shigo?” Daidai nan Anas yafito “waye ne Angel?” “Ummimi ce Ya Anas” apron d’in jikinsa yacire sannan ya k’ariso “ina kwana Anas” kamar wanda bare amsaba ya amsa “lafiya” tare da sake tare k’ofan dan kar ta samu daman shiga “wani abu ne?” “Breakfast na kawo muku.” “Ai da baki b’ata lokacinki ba we are making breakfast already zaki iya tafiya.” Hannu tasa ta taresa daga rufe k’ofan “Anas please karka min haka dan Allah” tayi maganan hawaye na ciko mata a ido daidai nan Fannah tafito daga d’akin sanye take da kayan bacci iya guiwarta, ganin alaman baquwa bakin k’ofan yasa takoma ta sanya hijabi sannan tafito “Habeebi meke faruwa anan?” “Ya Fannah Ummimi ce tazo.” Amal ta amsata. “Shine baku shigo da ita ba?” tayi maganan alokacin datake tsaye gefen Anas. “Ummimi please kishigo” wani kallo ta watsa wa Anas sannan tashigo da Ummimi ciki anan suka gaisa. “Waya miki kwatancen gidan namu?” “Tare da Ummie muka taho tana waje tana kuma gaisheku duka, dama breakfast na kawo muku.” “Allah sarki Ummimi da gajiya haka ai da baki wahalar da kanki haka ba, Anas d’an karb’i mana” yi yayi kaman be jita ba “Amal karb’i flask d’in kinji?” Ba gardama ta amsa takai kitchen hira kad’an suka tab’a wanda ciki ko uffan Anas be furta ba haka Amal ma kasancewar taga idon Anas daga k’arshe ma kitchen ya koma ya cigaba da abinda ke gabansa da Ummimi tazo tafiya takira Amal tare da miqa mata wasu hada’d’d’en porches na iphone 7s. “Gashi Habibti wannan naki ne naji Ya Anas ya siya miki iphone 7 koh?” Ta gyad’a kai “toh gashi bansani ba ko kinason maroon and red colour? best colorn Basmah da Barrah kenan I was thinking ko kema haka kinaso” amsa Amal tayi tana k’are musu kallo “sosai inason red and maroon colour Ummimi thank you.” “Always Habibti” ta bud’e mata hannu da nufin hug ba gardama Amal taje tayi hugging nata wani erin yanayin da bata tab’a tsintan kanta ciki ba tayi yau, tunda take bata tab’a jin dad’in hug ba kamar na yau gaskiyan Fannah our mothers are priceless sunjima a haka se kallonsu Fannah ke cike da jin dad’i ina ma Anas zebawa Ummimi chance d’innan ta zame masa uwa kamar yadda take buqata. “Toh zan tafi seko gobe in dawo kinji?” Amal ta gyad’a kai. “In na dawo gobe zaki bani labarin ki, kinga yanzu nasan favorite colors naki inason insan komai about you zaki min?” Shiru tayi chan ta gyad’a kai “thank you so much Amal Allah miki albarka yamuku albarka gabad’aya zan tafi” ahaka sukayi sallama. Dawowan Amal ta wuce kitchen “Ya Anas kalli porches da Ummimi ta kawo min na wayan daka sayamin amazing how tasan favorite colors d’ina koda shike tace favorite colors na step sisters namu Allah jik’an rai Barrah da Basmah ma kenan, Ya Anas Ummimi isn’t bad.” “Mesa kika karb’a?” “Ya Anas I’m sorry.” “Bance karki mata magana ba?” “Ya Anas she is our mother.” “Naji zan karb’i iphone d’ina se muga aina zaki sa porche d’in.” “Ya Anas I’m sorry.”*** ★★★★ Haka nan tun daga ranan Ummimi tacigaba da musu girki, da sauran ayyukan gida dukda abinda Anas ke mata hakan be hanata ja da baya ba saboda tasan dalilin dayake hakan alokacin data tafi shine me wayon chan dole abin yafi affecting nasa, addu’arta a kullum baifin Allah kawo ranan da Anas zeyi accepting nata as his mother ba, duk yadda yayi dan hana Amal alak’a da Ummimi yakasa as the saying goes ba a shiga tsakanin uwa da d’a, shak’uwa me k’arfi ne yashiga tsakanin Ummimi da Amal har fiye da nata da Shettima koda Amal takoma gida d’akin Ummimi ta tare, atare suke kwana da Ummimi, tamata tsifa tamata kitso har wanki haka ma Shettima tuni suka daidaita a tsakaninsu daman Abuu abinda yake jira kenan bayan ya tabbata everything is cool tsakanin Ummimi da yaranta ya dawo da ita d’akinta dad’i sosai Ummimi taji harda kukan murna her biggest dream is now a reality su Ummie da Fannah duk sunji dad’in wannan re union d’in har small party suka had’a inda Fannah tayi introducing Ummimi wa Maminta anan Ummimi taga Afrah in-law to be nata abinde se wanda yagani they turn out into a one big happy family banda Anas da duk wannan abubuwa da akeyi baima zuwa bale yaga kayan bak’in ciki har a yau bayajin ze iya yafewa Ummimi yariga ya dawo daga rakiyarta gabad’aya sede hakan be hana Ummimi fita daga harkansa ba ita ba. Musamman Abuu ya kira Fannah yamata godiya in person in da badan ita ba yasani da bare sake had’uwa da Ayshan sa ba, dabadan Fannah ba da Amal won’t get the chance to see her mother again, da badan Fannah ba da Ummimi won’t get the chance to see her family ever again har ta nemi gafararsu dan haka yayi mata godiya sosai tare sanya mata albarka ba iyaka. Shak’uwa na haqiqa ne ya cigaba da shigewa tsakanin Fannah da Ummimi, yadda Ummimi tad’au Amal haka tad’au Fannah tamkar ‘yar data haifa saboda irin ladabi da biyayyan da Fannah ke mata itama sekace wa Mami. Ummimi da Abuu dasu Shettima ne duk sukaje gidan iyayenta, alhamdulillah iyayen nata na nan da rai dakuma lafiya anan duk suka nemi gafarar Abuu akan abinda suka yi masa shekaru da dama da suka shud’e. Tun daga wannan rana rayuwa tayi turing perfect ma wannan family kan Ummimi da Ummie a had’e sekace ba in laws ba sosai Ummie kebawa Ummimi girma bata kuma dena yiwa Anas wa’azi ba itama fatanta Allah kawo ranan da Anas zeyi accepting Ummimi. Cikin Fannah se girma yake masha Allah a yanzu haka cikin nata ya tsufa yanada 8 months da sati d’aya, sosai cikin nata yayi girma yazamo ko k’wararren motsi zatayi setayi dagaske, ga wani erin tsoron haihuwan datake cikin yi a kullum ko asibiti bata son zuwa, Anas, Mami da Ummimi ke cikin kula da ita kullum, Amal tadawo zama dasu ma tak’i dan yadda batason rabuwa da Ummiminta bata tab’a sanin dad’in uwa ba se a yanzu. **** Yau ranar ta kasance Saturday zaune Fannah ke a garden tana d’an ciye ciyenta, gefenta Anas ne da laptop a gabansa yayi focusing sosai yana aiki akai. “Habeebi” takira sunansa. “Nagaji” “Yes Mom Hanan, Hanan na damunki ne?” Kai ta gyad’a a shagwab’ance. Laptop nasan ya rufe tare da ajiyewa kan table sannan ya matso kusa da ita yana shafa gashin kanta a hankali, “hak’uri kad’an zaki k’ara Sweetheart nan da 3 weeks in shaa Allah Hanan namu zata fito tadena damun min Flower” yayi pecking goshinta. “Yau zaki iya fita walk?” Kai ta girgiza mai da wuri “banajin zan iya fita yau Habeebi.” “Flower haka jiya mafa kika k’i fita kin tuna me Dr tace? Yi hak’uri kinji?” A hankali ya miqar da ita suka fita walk tafiya kad’an Fannah tayi tace ita su dawo gida hakan kuwa akayi.*** _3 weeks later 2 days later, exactly 9:43AM..._ Kamar yadda suka saba kwanciya manne da juna haka ma suke a yau sede Fannah ta kasa bacci tun bayan Sallan Asuba da sukayi, da k’yar ta miqe ta zauna dan girman cikin nata. Bayanta ke mata wani erin zafin azaba kamar tacire ta ajiye a gefe da na bayan ya lafa sekuma cikinta yahau juyi ta k’asa k’asa tun tana iya jure zafin takasa ta k’wala wa Anas kira a firgice ya tashi ganinta yayi miqe a k’asa tana hawaye tana juyi. “Omg! Flower what is happening?” kafin tayi magana ruwanta yayi breaking. “Anas I’m in labour please do something arrggh!” Ta saki k’ara hannunta na a k’asan mararta bayi yashige yayi brushing yafito da wuri da k’yar ya iya d’agata yakaita mota sannan ya d’ago maternity bag nata se asibiti, hankalinsa ya matuqar tashi ganin yadda Fannah ke kuka kamar ba gobe da k’yar ya iya tattara hankalinsa gu d’aya ya kira Mami ya sanar da ita, Mami ce ta sanar dasu Ummimi kusan a lokaci d’aya suka iso asibitin duka. Alokacin Anas na a d’akin da Fannah ke ya riqe hannunta gagam cikin nasa yana kissing kanta assuring her *_YANA TARE DA ITA_* sede sam its not helping sekaceba Flowersa ba gabad’aya tafita daga hayyacinta tana kuka tana ihu abin tausayi wane mutuwa zatayi, tana zufa yana share mata shima besan a lokacinda ya soma kukan ba sunfi minti talatin ana abu d’aya tun yana iya jure kukan nata har yakasa besan a lokacinda yafito ba he can’t take it anymore, bare iya jure pain da wahalan da Fannah ke fuskanta ba. Ummie, Ummimi da Mami ya tarar tsaye bakin k’ofan da gudu yayi kan Ummimi yayi hugging nata batayi tammanin hakan ba tsabagen yadda mamaki ya rufeta kasa hugging nasa back ma tayi. Kuka yake wane d’an yaro ya matseta gagam ajikinsa. “Ummimi I’m sorry, I’m so sorry please dan Allah kiyi hak’uri, please forgive me I never knew you went through this kafin kika haifeni nima dan Allah kiyi hak’uri for all that I’ve done to you, forgive me please mother.” *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [13:00, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💞* 9⃣7⃣ Hawayen jin dad’i ne suka soma tsiyaya daga idanun Ummimi tana meh godiya wa Allah azuciyarta, mahak’uri mawadaci, ayau ta tabbata wannan zance hak’urin ta be tafi in vein ba tunda finally Anas nata ya dawo gareta. Har a yanzu Anas be raba jikinsa daga nata bekuma bar kukan dayake ba, hannayenta ta aza a bayansa a hankali tare da sake tightening hug d’in “Alhamdulillah, Allah na gode maka daka dawo min da Anas d’ina, kabar bani hak’uri Babna ba abinda kamin is okay kaji? Stop crying.” “Its not okay Ummimi nasani I’ve been treating you bad har kuka na saki kiyi hak’uri dan Allah if only nasan kwatan abinda kikayi going through kafin kika haifeni believe me wallahi barin tab’a k’untata miki ba” yayi breaking hug d’in tare da riqo hannayenta cikin nasa “I’m truely sorry mother” a hankali ta raba hannunta daga nasa ta sa ta share masa hawayen da yakeyi “bakayi offending d’ina ba Babana, nice ya kamata nan in baka hak’uri. *I love you so much Anas.”* *“I love you too Ummimi you are the queen of my heart”* ya sake hugging nata dad’i sosai Ummie taji kamar ta cinye su finally! Anas yayi accepting Ummiminsa. “Babana ya condition na Fannah?” Ummimi tayi maganar cike da damuwa. “Ya condition nata please Anas” Mami ta mara mata baya wani sabon kukan yasoma musu wajen seda Ummimi tajasa kan kujera ta zaunar dashi “haba na miji dakai kake wannan kukan Anas gaskia beyi ba agaban Mami fah? Me kakeso tace? Surukin nata rago ne komeh? A’a gaskia bana so” tasa hannu ta share mai hawayen. “Kukan ya isa haka” “Ummimi I can’t watch her suffering like this, kuyi wani abu please.” “Zaka iya komawa ciki?” Da sauri ya girgiza kai “barin iyaba barin iya juran kallon Fannah tana shan wahala haka ba kuma ba abinda zan iya yimata to ease the pain ba, I can’t Ummimi.” “Shhh! Ya isa in shaa Allah zata sauk’a lafiya.” ta kwanto shi jikinta tana sbubbuga bayansa. Sede hawqyen da Anas yake yanzu ba dan Fannah bane, hawayen dayake na missing d’umin jikin mahaifiyarsa ne wanda ba abinda yakaisa dad’i a fad’in duniyan nan, bare iya tuna when last yajisa comfortable daga anriqe shiba se yau. *_our mothers are priceless lets respect them ba abinda zamu iya musu wanda zekai koda k’wayan zarrah ne daga cikin abinda suka mana. D’aukan ciki, rainonsa, haifan mu, shayar damu, tarbiyyattar damu d.s they’ve made alot of sacrifices just so to make us happy, they don’t give a damn in abinda zasuyi ze cutar dasu as long as it’ll make us happy toh zasuyi, Allah yabamu ikon kwantata masu so kamar yadda suka somu, Allah musu albarka ya saqa masu da gidan aljannah AMEEN_* _2 hours later..._ Anas ne tsaye akan Fannah data kasa haihuwa tin tin d’azu yanzu da labourn yad’an sauqa ne tasamu hankalinta, zufan dake akan goshinta yasa hanky ya share yana me mata sannu. “Flower I’m here kinji you can do this” kai kawai ta kad’a mai. “Habeebi I can’t barin iya ba.” “Sure you can Sweetheart” yayi pecking goshinta. “Please karka sake tafiya kabarni Habeebi stay with me please.” ta sake matse hannunsa dake cikin nata tana hawaye. Badan yanaso ba ya gyad’a mata kai alokaci guda labour natan yasake hitting nan aka shiga new chapter again ihu da kukan da take yafi nada data wani damk’o Anas seda ta yayyak’ushe shi da zafin yazo yayi mata over batasan a lokacinda tafara ja mai Allah ya isa ba duk yana ji yasan ba’a cikin hankalinta take ba se sannu yake mata chan ma tace yafita mata daga d’aki batason sake ganinsa haka sukayi spending numerous hours cikin labour room suna abu d’aya. _3 hours later exactly 3:20PM_ Bayan azaba da wuya da kuka da zagi da yak’ushi Flower tasauk’a lafiya tasamu ‘yarta wacce take nan tubarkallah. Wani irin nunfashi ta saki, seji take kamar an sa mata sabon rai, “Flower you did it, Hanan is finally with us” yayi pecking nata a goshi “thank you so much Sweetheart Alalh miki albarka for this blessing I love you so much.” “I love you too Daddy’n Hanan, I love you so much” tayi maganan da murmushi kwance akan fuskarta. Daidai nan nurse ta miqo ma Fannah Hanan dake weighing 6 pounds, lullub’e take cikin pink shawul kamar a saceta a gudu. Yarinya k’atuwa tubarkallah, farinta da kamanninta sak na Daddy’nta yanayin gashinta kuwa koba a tambaya ba ansan na Mammynta ne, gashi har kan goshi da kuma kumatu ruwan zamzam da dabino Anas yabata how cute and adorable suna kallon Hanan insu, daga nan Anas ya amshe ta “Flower this is just my carbon copy ana cewa muna kama da Amal but not as we do da Hanan I love our baby Flower most of all I love you.” Murmushi tamasa “you’ve once promised me ni zanyi naming baby’nmu ko?” “Yes Flower and zan cika promise d’in yau gata kiyi mata hud’uba” amsar ta tayi ta mata wasu maganganu a kunne sannan a fili tace, “Allah raya mana AYSHA.” Cike da rashin fahimta Anas ke kallonta “Aysha kuma Flower? Kin fasa Hanan? Your dream name?” Kai ta kad’a mai ko kad’an “My Lion sunanta Aysha takwaran Ummimi but na mata alkunya da Hanan dashi zamuna kiranta ka gane?” “Dagaske takwaran Ummimi ce?” “Yes Sweetheart.” “Wow! this is great news Allah raya mana mahaifiya ta” duk sukace “ameen” sede wani gudu ba hanzari ba kan Fannah ya d’aure ta d’au Anas will freak out inyaji batun sunan amman kuwa se gani take kamar ma yafita jin dad’in sunan Hanan. “Habeebi kasani cikin rud’ani, nad’au barakayi accepting asalin sunan Hanan as Aysha ba.” “Mesa barinyi ba Flower bayan Ummimi mahaifiya ta ce, kamar yadda kika sha wahala kafin kika samu Hanan haka nima tasha kafin ta sameni, I never knew haka mothers namu suke shan wahala da ace inada masaniya akai wallahi da ko na second barin tab’a b’ata wa Ummimi rai ba, kamar yadda barin bari for once Hanan ta miki ba daidai ba nima barin sake yiwa Ummimi ba daidai ba I’ve asked for her forgiveness earlier we are all good.” dad’i sosai taji maras misantuwa. “Dasgaske Habeebi?” Ya gyad’a mata kai. “Today is indeed the happiest day of my life Habeebi, kai da Ummimi kun shirya ga zuwan Hanan omg! I feel like a queen” daidai nan Hanan tad’an yi miqa tare da bud’e idanunta se gasu nan blue sak erin na Daddy’nta atare sukace “she has blue eyes too.” sekuma suka murmusa. “Habeebi Hanan nada blue eyes.” “Yes Sweetheart mena had’a rai kuma Flower?” “Eh mana ni insha wahala in haifeta kuma ta d’au kominka, farinka, face naka eyes naka ni kawai gashi na ta d’auka.” “Ohh common Flower nan gaba kika sake haihuwa masu kamanninki zaki haifa in shaa Allah.” “Wa ze sake haihuwan? Ni? Chab!” “Eh mana we will have like 10 kids.” “Engine d’in yara ka miyar dani ko meh?” “LOL but jokes apart we will have like 4-5 kids ba? Please say yes Flower.” “Muddin you’ll be the strong Hyena I know we can have like ten kids in kanaso” tayi maganan tare da kashe masa ido daidai nan Ummie dasu Mami suka shigo Ummimi ce a sahun gaba ita ta fara amshe Hanan “wow tubarkallah sannu fa uwata” nan tasa mata albarka sannan ta miqa sauran suma sekuma sannu da sukayi wa Fannah wanda ya biyo baya. “Ummimi ga Aysha fa.” Cewar Anas. “Aysha kuma aina?” “A hannunki” Fannah ta amsata. “Kai tun ayau na zama kaka kun fara min tsiya wato koh?” “Am serious Ummimi Fannah named our baby after you sunanta Aysha but za’a na kiranta da Hanan.” “Ummimi kar kijisa mu biyu mukayi shawaran muka bata sunan kuma ma shi ya fara kawo shawaran.” Hawayen jin dad’i Ummimi ta soma “barin iya muku godiya ba Anas da Fannah, addu’a na d’aya ne Allah ya barku tare, ya k’ara k’arfin soyayyan dake tsakaninku yacigaba da kawo mana zuriah d’ayyyiba yakuma raya mana Aysha me suna na” duk suka amsa da ameen. In next Flower ta samu twins kuma Ummie da Mami zamu sa ko Flower? Ta gyad’a mai kai tana murmushi. “Wai Anas akwai son baby girls inkuma maza ta samu fah?” cewar Ummie su Mami se dariya suke. “Fine se asa musu sunan Baba dana Abuu.” Allah kawo masu albarka Habibti Mami tayi maganan tana shafa kan Fannah. Ameen Mami I love you” “I love you too” Anas ganin haka yayi gun Ummimi da Ummie shima tare da hugging nasu all “I love you momies. Kin d’au ke kad’ai kike da mama ne anan?” Ya juyo yana kallon Fannah kaman d’an yaro “naki d’aya ne nawa har biyu infact har uku tunda ga Hanan.” Duk suka kwashe da dariya banda Fannah dake dariya kad’an kad’an dan azabah. _some hours later... A gidan Mr. Fauzi_ “Ummimi wai ina zaku kai kayakin Flower ne?” “D’akinta chan zata koma da kwana har se ta fita daga arba’in.” “WTF!” Yayi exclaiming ba tare da yasan lokacin daya fad’a hakan wa mahaifiyar saba. “Meh kace Anas?” Ta zaro ido cike da mamaki. Kai yasoma sosawa “I mean Where’s The Fork da Amal tashigo dashi d’azu?” “Zakamin irin na Yusuf kenan kad’au bansan meaning d’in WTF d’in bane koh? What The Fuck ko ba haka ba?” Kallon Ummimi yake cike da mamaki sekuma ya tuna tayi zaman tsawon 14 years a k’asan turawa dole tasan abubuwa irin haka. “Uhmmm” yasoma shafa gemunsa “Ummimi please kubarta anan.” “Kamar ya abarta ne wai Anas?” “Muna kwana tare.” “Chankwad’i!” Tayi maganan tana tafa hannayenta “katab’a jin inda mace ta haihu takuma cigaba da kwana da mijinta? Dan ma Mami batace zata kaita chan gida suyi arba’in ba kenan kake wannan magana.” “Haba mana Ummimi please kubarta anan” da k’yar d’in k’yar Ummimi ta shawo kan Anas ya yarda Flower takoma d’akinta badan yanaso ba dan Ummimi keso. (Mother’s Love) Haka nan tun daga ranan da aka samu Hanan akayi limiting tarayyan Anas da Flowersa abin har rashin lafiya yakeson sasa shida ya saba kullum tare da Flowersa yau an rabasu na k’arfi da yaji a wuni befi su had’u na ‘yan mintuna ba, abin damunsa yake sosai ga yadda dangi daga Bama suka rik’a zuwa suna zuba k’auyenchi a gidan. Ahaka har Allah yakaisu ranan suna inda dangi da mutan arziki suka halarci bikin sunan Hanan. True fans na *_TANA TARE DA NI_* dam cikin gidan Mr. Fauzi musamman ma ‘yan *_MIEMIEBEE NOVELS GROUP_* se zuba k’auyenci suke gun security door kowa tace se k’ofa ya kira sunanta haka sukasa Amal agaba tana registering sunansu. Su Mrs Shamsur ne a b’angaren kitchen ansha bidirin suna wane na bikin aure kowa yasan Mr. Fauzi da son kashe kud’i ba sena tsaya lisafo abubuwan da akayi a bikin sunan ba ande ci uwar naira thast all (LOL) anchi, ansha anyi pictures, Fannah da Baby Hanan nata sun ci gifts ba dama. Tunda Fannah ta haihu Ummimi da Mami ke kanta, Ummie na achan gida dasu Abuu sede in ta wuni musu takoma, su Amal anzama Aunty rawan kai ya k’aru a yau Ummimi ta koma gida itama, ya rage Mami kad’ai ita kanta Fannah missing Habeebinta take ji take kamar taja 40 days d’in yayi ya k’are takoma gun Lion nata. Kamar yadda al’ada ya tanadar seda Fannah tayi 40 days cur! Sannan Mami ta barta takoma d’akin Anas a ranan itama Mamin takoma gida aka ragar da love birds zallah. _4:25PM_ Daidai dawowan Anas gida daga office kenan meetings hud’u yayi attending yau he is all tired k’ofa na bud’uwa yaga Fannah da Baby Hanan nashi tsaye behind it tasa wani red flow lenth gown me siraran hannu wanda yasha ado sosai, kamar yadda take sanye da jan kaya haka ma tasa wa Baby Hanan jan ‘yar kanti da white socks seda white head band se k’amshi ke tashi a jikinsu take wajen Anas yanemi gajiyan daya tattaro daga office ya rasa ko be tambaya ba yasan Mami ta tafi dalilin dayasa Fannah tafito kenan. “Welcome home My Lion.” Ta fad’a tana mai murmushi. K’arisawa ciki yayi ya amshe Baby Hanan tare da kissing nata passionately sun d’au tsawon loakci suna abu d’aya sannan a sannu tayi breaking kiss d’in. “I missed you” suka furta wa juna sekuma suka murmusa. “Flower you are looking extra ordinary beautiful I mean you and Baby Hanan.” “Thank you Honey, muje kachi abinci” tayi maganan tare a karb’e masa jakar laptop nasa sannan suka nufa dining tayi serving nasu, Hanan na a hannunsa har suka gama cin abincin. “Flower amman bake kikayi girkin nan ba.” “Why do you ask?” “Sabida I know girkin Ummimi ne wannan.” Habeebi ba’a iya maka wayo just like Hanan kasan d’azu dana mata wanka na shayar da ita har ta fara bacci fa ina cire maman daga bakinta ta tashi tasoma kuka koda nasa mata sucker nata tak’i sucking sabida tasan ba nono bane, you two ba’a iya muku wayo.” “Team Blue Eyes kikeji” nan yad’aga Hanan sama yana mata wasa. “A’a Habeebi a hankali please kasan she is still a baby.” “Toh Mom Hanan nida bansan zafin haihuwa ba se a fad’amin magana.” “LOL its the truth ba abinda yakai haihuwa azaba Habeebi.” “I know Babe tunda har kika jamin Allah ya isa kam ai komai ya b’aci.” “I said I take it back kaima kasan cikin hayyacina barin tab’a ja maka Allah ya isa ba Daddy’n Hanan.” “Nima wasa nake gobe tare zamuje office.” “Kai dawa?” “Me, you and our Hanan, dama jira nake Mami ta tafi mufara zuwa tare ‘cause I’m missing you guys like hell.” “In Ummimi ko Mami sukaji na bika office kaima kasan da akwai k’ara’i.” “Bawani k’ara’in nan you are my wife and this cutie over here” yayi kissing kunatun Hanan “is my daughter whats there? Final discussion gobe zamuje office tare.” “Yes Sir” ta fad’a tana mai murmushi anan sukayi d’aki. *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [13:04, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* 9⃣8⃣ *A/N* *Dear Supporters (fans) barin che dear readers ba dan kuwa dayawa suna karanta wannan littafi nawa suna min hassada akai, wasu kuma suna zagina akanshi ba gaira ba dalili, anyways ina me farin cikin sanar da masu min unnecessary k’orafi akan wannan littafi nawa, wannan shine second to the last page of the story, Allah’n daya had’a mu shi ze rabamu, wataran zaku nemen danku zagen ma baraku sameni ba dama shi had’uwan social media haka yake. Dayawa daga cikin readers harma writers sun b’ullo ta duk inda suka san zasu iya dan hanani cigaba da wannan labari nawa amman dake nasan masoya na sunfi maqiya na yawa sesa ban d’aura kowacce aka ba na cigaba da abinda na fara, true fans kusani ko badan saqonnin alkahirun da kuka riqa mani ba, tsoronku wai kar nayi fushi na katse labari na inason kusani wallahi ba’ayi wacce zata hanani k’arisa abinda na fara ba. I just want you guys to know that no matter what *_INA TARE DA KU kamar yadda kuma kuke TARE DA NI_ Allah shige mana gaba.* *Babban albishir danakeson ma supporters d’ina shine page 98 of *_TANA TARE DA NI_* *is dedicated to each and everyone of you for the love, support and care I recieve anytime I turn on my data* *ina fatan yin hakan ze sanya ku nishad’i dakuma jin dad’i kamar yadda lovely comments naku ke sanya ni jin dad’i nima. MIEMIEBEE loves you so very much!!!* ___________________________________ Washegari suka shirya tsaf suka wuce office, duk meetings da Anas yake dashi dakuma appointment dayake dasu da mutane yayi cancelling ba abinda ya tsinana a office d’in ranan se soyewan da suka tayi da Flowersa dakuma wasa da Hanan, sun d’au selfies ba iyaka bayan sunchi lunch Hanan tayi poopoo aikin da Fannah ta tsana kenan wanke kashi, ko time da Aiman ke baby haka take kwana-kwana in Mami ta sata yi. “Habeebi Hanan tayi ajiya.” “Toh meh aciki? Kowa nayi.” “Nikam...” Ta turo baki wipes na hannun nata ya karb’a cike da mamaki take kallonsa “Habeebi meh zakayi?” “Zan goge mata mana.” “Ka iya ne?” “Zauna kiga.” Akan matress na ta ya kwatar da ita sannn yacire mata pampers d’in yayi disposing sanan yayi using wipes d’in ya gogeta tatas yasake sa mata new pampers kallonsa kawai Fannah ke she can’t be happier than this duk wani abinda tasani Anas nata ya iya she’ve got the best man! Se dariya Hanan ke ma Daddy’nta dayake sa mata new pampers bayan daya gama ya d’agota yana nunata da wa Fannah, “ya kika ga?” “Habeebi kasan ban tab’a ganin amazing person like you ba komai ka iya zamuyi deal kai zaka na wanke mata poopoo in tayi nikuma zannayin sauran.” “Niko duka ma kika ce zan nayi barin damu ba because I love my little Fauzi” yayi pecking Hanan a kumatu daidai nan wayar Fannah yasoma ringing tana kai dubanta taga Mami. “Omg! Habeebi yanzu me zance mata? Nasan definately tana gidanmu ne yanzu haka seda nace maka kar muzo kace se munzo.” “D’aga yanzu muji” ba gardama ta d’aga “hello Mami?” “Eh Fannah gani a gidanku fa ina kika jene?” “Erm.. Erm..” Ta hau kame kame. “Daga tafiya na kin kama yawo koh?” “Mami ba yawo bane fah” ta kare wayan da hannunta “Habeebi meh zance mata?” Amsar wayan yayi “Hello Mami ina wuni?” “Lafiya Babana kuna tare da Fannah ne?” “Eh mun fito asibiti ne d’auka wa Hanan allura.” “Ohh okay toh dama tuwo na kawo wa Fannah zan ajiye mata seka fad’a mata.” “Okay Mami mungode.” “Yawwa ashafa min kan jikata.” “Toh anagama se anjima” karap ya katse. Pecking nasa tayi a gefen idansa “Mr. Fauzi can tell lies ehm!” “LOL ai da nayi shiru ta sissileki.” “Ai cemata zanyi kai kace in biyo ka.” “Haha! Zan qaryata ki ince kekika dameni wai sekin biyoni.” “Allah ko?” ”Yes Baby d’an had’a min coffee kinji I can’t remember when last nasha coffeen Mrs. Fauzi.” “Barin had’a ba” ta murgud’a mai baki. “Flower menayi kuma yanzu?” yana tab’a hannunta taja da baya. “Bansani ba ni miqo min Hanan in bata lunch nata.” “Zo ki bata anan yi hak’uri Mom Hanan” a hankali ya jawota ta zauna agefensa sannan ta amshi Hanan tafara shayar da ita yana zaune gefensu yana kallon su cike da adoration**** ★★★★ Life couldn’t be better, Anas, Fannah da Hanan nasu rayuwa na tafiya masu daidai se girma Hanan take wane kazan agric, tana girma tana kyau tana kuma sake kama da Daddy’nta, a yanzu haka Hanan nada 5 months tafara zama, yarinya son kowa k’in wanda ya rasa sede Fannah bata shiga da ita cikin jama’a ba kowa so yake ya karb’eta. _Mother’s day 8th May 2016 4:10PM A GIDAN MR. FAUZI_ D’an rumfa ne wanda k’ark’ashinsa su Ummie, Ummimi, Mami dasu Afrah da kowa da kowa ke zaune akai. Tun jiya Anas yaketa preparation na wannan babban rana he want to make Ummimi feel special on this special day. Atare Fannah dake riqe da Hanan a hannunta suka fito da Anas tasha wani purple lace wanda yayi fitting nata sosai, purple kaya tasawa Hanan ma, kullum haka suke suna anko. Wajen da Anas ya tanadar mata ta zauna sannan Anas yayi welcoming kowa da kowa wani k’atoton cake aka shigo dashi aka ajiye a tsakyan d’an taron daidai gaban Ummimi kenan da *HAPPY MOTHER’S DAY* rubuce akai. _“Ummimi on this special day I your son Anas, Shettima my brother and Amal our sister will love to show our love for you, thank you for being there for us all the time we love you so very much thank you for being the perfect mother”_ ya miqa hannu ya d’agota daga kan kujeran da take zaune. “And all the other mothers here, Mami, Ummie and my dear wife Fannah Happy Mother’s Day” nan duk suka mimmiqe sukayi cutting cake d’in sannan Anas yayi presenting gift nasa wa Ummimi, se Ummie se Mami haka duk sauran ma sukayi lastly yakai wa Fannah wani d’an medium sized cake da *I LOVE YOU MAMMY (HANAN)* rubuce akai “thank you Habeebi.” “Always Flower this is from Hanan ita tace in baki so thank her not me” murmushi ta saki sannan tayi pecking Hanan a lips. “And this is from me as a token of appreciation da kula mana da Hanan da kikeyi” amsa tayi ta bud’e white diamond ne aciki na d’an kunne d sarqa aciki. “Habeebi this is too much.” tafad’a disbelievingly. “Its not Flower because I love you.” ”I love you too.” Nana suka ci kuma sukayi wasa da cake suka b’ab’b’ata jikinsu, sunyi having fun like never ba k’arami ba yaro duk suka zage suka ta wasa daga k’arshe Ummimi tasamu Anas tamasa godiya sosai in person. *RAYUWAN HANAN* Dan nishad’i. _2 years later..._ Hanan an zama ‘yan mata fa yanzu tana da 2 years 5 months yanzu se uban surutu da rashin kunya kullum suna cikin fad’a da Fannah, Allah Allah Fannah ke asata a school tayi tayi da Anas yasata koda a pre school ne Anas yak’i acewarsa se Hanan takai 3 years tukuna. Badan komai Fannah keson asa Hanan a school ba illa dan ta huta daga headache da Hanan kesa mata, gashi bata san me ba duk abinda Hanan ta mata bata iya dukanta saboda yadda take son ‘yarta. Yau ranar ta kasance Tuesday k’arfe shidan da Fannah ke tashi dan ma Anas breakfast Hanan ke tashi itama sekace me alarm Fannah ta rasa ya hakan ke faruwa na farko bawai a d’aki d’aya suke kwana ba amman sede bata tashi ba Hanan ma seta tashi tana fitowa daga d’akinsu ta tarar da Hanan tsaye bakin k’ofan d’akinta da babban pink teddy bear nata da tsayinsu d’aya riqe a hannunta d’ayan hannun kuwa ribbons na kanta ne wanda da alama pincikesu tayi. “Good morning Mammy.” tace cikin siririyar muryarta me uban sauri. Gabanta Fannah ta nufa ta tsuguna “Good morning baby, Hanan sweetie yanzu kitson dana miki jiya kika warware duka? Ina sauran ribbons d’in?” Baki ta turo tayi nuni da d’akinta. “Sweetie mesa kika tsefe? Bana ce miki karki tsefe ba?” “Banacho! I want a new one.” ”Allah ka rufa min asiri!” Fannah tayi maganan tana kallon sama, “koma d’akinki ki kwanta kokuma kije kisamu Daddy a d’aki” tayi maganan tana kama mata dogon sumanta gu d’aya. Kafad’a Hanan ta buga ”ni jan biki kitchen.” “Saboda ki sake fasa min plates ba? Banaso koma ki kwanta” tana kaiwa nan ta nufa kitchen Hanan na biye da ita. Kaman dagske Hanan ta ajiye teddy nata a gefe ta d’alle kan kujera tana kallon mamanta na aiki chan ta miqa mata wuqa ganin Mammyn nata ta d’au albasa. “Good girl” Fannah tayi praising nata. Sid’ak sid’ak Hanan ta wuce store room taciro bucket da moping stick ta cika da ruwa sannan tajawo shi kitchen, inda ake ajiye morning fresh ta nufa tajuye roba d’aya ciki duk anan Fannah batasan me Hanan keyi ba as she is busy cooking. Yadda Hanan taga cleaners keyi itama ta soma mopping kitchen d’in Fannah na juyawa dan d’auko abu taga Hanan na mopping kafin tace Hanan bari aikin gama ya riga ya gama Hanan ta juye ruwa kusan rabin bucket a k’asa. “Aysha Hanan Fauzi!!! Yau sena zaneki a gidan nan” da gudu ta yi d’akin su taje ta d’ale jikin Anas anan shima ya tashi. “Daddy talk to Mammy wai seta min duka.” “Duka kuma?” ya maido da kallonsa kan Fannah. “Metayi kuma Flower da zaki ce zaki daka min little Fauzi?” “Habeebi ruwa kusan rabin bucket ta zubar a kitchen.” “Toh shine abin tada jijiyan wuya?” “Dama ai nasan haka zakace Hanan ki nutsu tam! Asata a school kak’i an bar yarinya se uban gagara oh ni Fannah zaki kasheni wallahi.” “Oya Hanan say sorry to Mammy.” “But Daddy..” “Shh! And say sorry.” “I’m sorry Mammy” tayi maganan hanneyenta riqe da kunnuwanta “barin sake ba.” “Allah sa Hanan” tana kaiwa nan takoma kitchen. ****_Some minutes afterwards..._ “Habeebi baraka tafi office da Hanan ba yau?” Fannah tayi maganan tana bottling wa Hanan shirt nata. “Inada very important meetings yau bareyi inje da ita ba gobe in shaa Allah zamuje ko little Fauzi?” “Yes Daddy!” ta fad’a tana jin dad’i. “Oh ni wallahi toh kaja mata kunne karta min gagara yau kuma karta shiga harkan cleaners.” “Who is a good girl?” “Aysha Hanan Fauzi!!” Hanan tayi maganan tana jin dad’i. “Good banda disturbing Mami kinji?” “Yes Daddy” Fannah na gama sa mata kaya taje tayi hugging Anas. *** _3:15PM_ Zaune Fannah ke akan gadon d’akinta daidai tagama ciro wa Hanan kayakinta daga drawer kenan. “Hello Habeebi ina jinka kace Moosa zezo?” Tayi maganan wayanta maqale a kunneta. “Eh zezo seki basa files dana bari akan gado earlier d’azu.” “Oka-” bata samu daman k’arisa maganan ba takira sunan Hanan da k’arfi “Haanaaan! Nooo!” Ai bata k’are maganan ba Hanan ta ture duka jeren da Fannah tayi gaban dressing mirron abinda ya kama kan turarukanta man shafawa komai da komai. “Hello Flower what is it?” Anas yayi maganan cike da tashin hankali acewarsa abu ne yasamu Hanan. “Habeebi wallahi yau sena zane Hanan.” “No please don’t metayi?” “Baraki matsa a wajen ba sena iso tukuna koh?!” Fannah ta tsawata mata, jin haka Hanan tabar d’akin ma gabad’aya tasa gudu da wani baby pink overall dake jikinta ta wuce nata sannan taje ta fara sabon b’arna achan, bin pages na story books nata take tana yayyage su one by one tana littering d’akin nata dasu. “Jeren dressing mirror na fa ta ture kap a k’asa.” “Flower please karki tab’ata.” “Wallahi Habeebi kabarni da ita” da k’yar Anas yayi convincing Fannah ta hak’ura. **** Hanan de ba wanda yasan ranan shiryuwanta gagaran yau daban na gobe daban Fannah tayi magana har tagaji batasan kuma me zata sake yima Hanan ba kotace zata bugeta bata iyawa, yanzu sede in Hanan tayi b’arna kawai ta kalleta ta kad’a kai tace Allah shiryeki yarinya kuwa ta amsa da Ameen Mammy tana mata murmushi nan kawai se Fannah taji ta huce. Akwai lokacin da ta kama Hanan da wuqa da albasa a kitchen ita wai a dole zata yanka albasa. Sede in Hanan bataga bayi a bud’e ba se ta saci jiki ta shiga takuma kulle da key sannan ta bud’e tap na jacuzzi ta cikasa dam da ruwa harya fara yoyo a k’asa, ita Fannah tsoronta ranan da Hanan zata fad’a cikin ruwan. Hanan nada shekara uku aka sata makaranta dad’i kaman ya kashe Fannah finally zata huta itama first day of Hanan a school ta koyo rubuta letter A believe me gidan Mr. Fauzi gabad’aya seda aka zana da capital letter A and Small letter a. Anas na dawowa daga office kafin ya shigo gida yaga letter A na masa sallama jikin k’ofa koda ya gwada gogewa kuwa bai goguwa kasancewar da permanent marker tayi rubutun tunanin ina tasamu ya soma chan ya tuna ashe jiya a gabanta ya miyar da markern bayan daya gama rubutu dashi. Bayan k’ofa ya bud’u masa ya shigo yaga a kan marble floor na parlourn ma an rubuta Aa baki ya tab’e sannan ya shiga kiran sunan ta. “Hanan! Daddy is home” alokacin Fannah na a d’akinsu tana baci itako Hanan tana d’akin Fannah taje ta bud’e drawer tacicciro ninkakkun kayakin Fannah tana hargitsa su fuskarta kuwa janbaki ne ko ta ina har akan girarta tana jin muryan Daddy tasoma k’ok’arin cire bangles da sark’ok’in Fannah datasa a wuyanta dakuma hannu sede kafin tagama cirewa Anas yashigo ya kamata. Murmushi ta hau mishi “Daddy!” “Omg Hanan what have you done?” Yayi maganar yana bin d’akin da kallo k’aran zuban ruwan daya keji a bathroom yasa yayi sauri ya bud’e ya duba, jacuzzi ya tarar cike dam da ruwa da sauri ya rufe yafito. “Little Fauzi ban hanaki tab’a kayan Mammy ba?” “Daddy you did” ta had’e rai. “Toh mesa kike b’ata mata kaya?” In kaiki amiki allura ko?” Dagudu ta je takama k’afansa “no Daddy nadena.” *© MIEMIEBEE* beeenovels.blogspot.co.ke [13:09, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💞* 9⃣9⃣ *THE END* “Little Fauzi kinsan in Mammy taganki zata zane kikoh?” “Daddy hide me” tasake matse mai k’afa, hannu yasa ya d’agota sama yana k’are wa jan bakin dake fuskarta kallo kawai seya hau dariya, hannu tasa cikin dimple nasa tana matsewa itama se ta gwada tab’a nata. “Makeup artist indeed why are you being stubborn kinason mu fara fad’a dake?” Ta girgiza mai kai “toh karki sake tab’a kayan Mammy kinji? Duk wanda yake sa Mami magana fa ojuju zasu kama shi irin na cikin story books naki.” “O’o Daddy nadena.” “Who is a good girl?” “Aysha Hanan Fauzi!!” “Great! High five!” Suka tafa hannu a sama “low five” suka yi a k’asa “then friendly punch” sukayi punching juna a hannu, kayanta ya cire mata ya nufa bayi da ita ya mata wanka da k’yar ta yarda yafito da ita dan shegen son wasa da ruwa ne da ita, kayakin Fannah ya hau tattarawa ya ninke ya miyar cikin wardrobe d’in da sauran accessories nata. “Ina Mammy?” “She is sleeping” ta basa amsa tana k’ok’arin ciro d’aya daga cikin hand bags na Fannah dake rataye a hanger. “A’a little Fauzi banda b’arna zo na saya miki chocolate” da gudu tayi wajensa bekaita ko ina ba se wajen data yi rubutu “Little Fauzi what is this?” “Wannan?” ta nuna mishi da yatsa. Kai ya gyad’a mata. “Daddy bakasan capital letter A and small letter a ba? Aahhh! Shame on you” Tasa hannu tana tare kumatunta. “I mean mesa kikayi rubutu ajikin k’ofa da nan?” “Aunty said we should practice everywhere.” “Hanan what she meant is that kuyi practicing a books ko papers ba jikin walls, floors da k’ofa ba, ba’a rubutu ajikin bango kinji? A book kad’ai akeyi.” “O’o nafison anan my book is too small.” Da k’yar yayi convincing nata ta yarda barata sake rubutu ba se cikin littafi dukda kuwa yasan baji zatayi ba. A 2 seater ya zaunar da ita ya kunna cinema yasa mata Cartoon network wai a tunaninshi cartoon ze d’auke mata hankali baratyi b’arna ba dan ze shiga bayi watsa ruwa, “Behave yourself kinji little Fauzi? Banda tab’e tab’e.” “Yes Daddy” tayi maganan tare da sake riqe teddy bear nata tana mai murmushi yana b’acewa daga kallonta ta sauk’o kan kujeran ta d’au remote tasoma bin buttons d’in one by one tanaci seda ta cinye kap sannan ta miyar ta ajiye ta nufa dining ita wai a dole yunwa takeji zata d’iba abinci. Flask d’in ta bud’e taga spaghetti seta sakar da murmushi ta fara bin kan naman ciki one by one tana chi kad’an ta rage agarin rufe flask d’in tayi b’arin abincin duka ya zube a k’asa. “Oh no! Mammy will beat me today, Aunty said learn to tell your parents sorry when you are at fault” cute smile nata ta sakar sannan ta ja teddy bear nata ta nufa d’akinsu Fannah a hankali ta bud’e k’ofar ko noticing nata su Fannah da suka zurfafa suna kissing juna basuyi ba, baki wangalau Hanan ta sake, a nitse ta dosa cikin d’akin taje ta zauna kan couch opposite them tana kallonsu, har a ynzu basu san da shigowarta ba seda Anas ya juya Fannah, Fannah taga Hanan ko kad’an shi Anas ma be ganta ba. “Habeebi wait! Ka tsaya Hanan is here” firgit ya miqe zaune yana k’ure wa Hanan data sa hands nata a both side of her cheeks tana kallonsu ko kyafta ido babu. Dukansu were at shock bawanda ya iya mata magana gawani kallonsu da take har yanzu. “Little Fauzi why didn’t you knock before you came in?” “Because the door was open, Mammy what are you doing with Daddy?” Cike da kunya Fannah tace, “nothing sweetie jeki d’auko min princess gown naki mu nuna wa Daddy.” “Saboda in na fita ku sake kama junanku ba, hmm bad girl” “Little Fauzi don’t say that kinga Mammy batada lafiya ne nake dubata.” “Are you a doctor? Toh aima you may kill her kayi nauyi ka zauna akanta.” “Ya Salam Hanan dan Allah kiyi shiru kuma karki sake magana haka, we are sorry kinji?” Cewar Fannah. “Perfect! Dama nima nazo ince miki sorry kuma kin fad’a min thank you Mammy’ tayi tsalle ta sauqa daga couch d’in. “A’a wait Hanan what did you do?” “Nothing Mammy, Daddy ka cigaba da duba Mammy bye” taja musu k’ofan. **** Chan dare around 7:30PM su Fannah suna zaune a parlour, Anas is busy with work itakuma tana taya Hanan homework sede sam Hanan tak’i concentrating. “Daddy Mammy our teacher has a veryyy biiggg nose.” “Ikon Allah Hanan me ruwanki da hancin teacher’nku kuma.” “Mammy baki gani bane? Ai seda na gwada sa 5 fingers d’ina aciki kuma duk suka shiga kuma setacmin wai you this Aysha you’re so stubborn you are lucky your dad is... Is.. Billo oho ni na manta haka de tacemin.” Dariya sosai Anas ya tsaya yi. “Habeebi Allah kadena mata dariya the more kana mata dariya the more take sake rashin ji.” “Flower I can’t help it.” “Flower??” Hanan tayi maganan tare da tab’e baki “Daddy mesa kake cewa Mammy Flower? Flowers fa acikin story books suke” shiru kawai yamata dan kuwa Hanan tafi k’arfinsa bayan sun gama mata home work d’in da k’yar, Anas yace, “Hanan baby miqo min remote” “Daddy gashi” daidai ze danna power button kenan yaga wuyam! Hannu ya aza kan bakinsa in shock. “Hanan Fauzi! What is this? Ina kika kaimin buttons d’in? “Daddy bani bane.” ”You are lying ko? Then waye ne?” “Mammy ne naganta d’azu tana ci but don’t tell her” aiki Fannah dake fitowa da towel na Hanan ta jiyota. “Hanan nice nachi remote?” “Eh kece.” “Oh Allah shiryeki Hanan.” “Ameen Mammy kema Allah shiryaki.” “Ai ka soma gani da kanka ni wuce muje mu miki wanka ki kwanta gobe akwai school.” “O’o ni barin sake zuwa ba hancin teacher’n mu is too biggg.” “Oh ni Maman Hanan da ana siyar da mutane dana siyar dake Hanan in huta.” “Kema Mammy da ana siyar da mutane dana siyar dake.” Hanan ta kwaikwayeta. Anas na tashi shiga d’aki dan d’auko wani abu Hanan ta kewaya taga ba Fannah tuni ta nufa gun dataga papers na Anas “aha! Daddy said we only write in books and on papers” biron dake kusa da wajen ta d’au tahau zana ‘Aa ’ masu desings akai, fitowan Anas yayi daidai da lokacin data ke danne danne cikin laptop nasa. “Daddy does like this and like th-” “Omg! Little Fauzi Allah yasa baki fitamin daga inda nake ba saboda banyi sav-” aiko be k’are maganan ba yaga tayi shut down na system d’in gabad’aya. “Hanan” ya juyo yana kallonta cute smile nata ta sakar masa da innocent baby face nata. “Daddy!” Kafin yamata magana ta d’au files na F&C enterprises da suka basa dan signing meze gani akai? ‘Aa’ na Hanan akai kota ina baki yasake totally speechless “Flower!” Ya danna wa Fannah kira ”yes Habeebi” tayi maganan tana fitowa daga kitchen. “Kizo ki d’auki wannan b’eran kisata baccin dole please.” “Yau kuma kanku akeji da little Fauzi da bata laifi? Hanan me kikayi wa Daddy?” “Be iya rubuta A bane na mishi kuma d’azu yace I should stop writing on doors and walls I should write on on papers and in books shine nayi.” ★★★★ _6 months later..._ Tsaye Fannah ke a kitchen tana girki da k’atoton cikinta wanda yake nan kaman na twins na 5 months, aiko Hanan ta tabbatarmin da eh cikin ‘yan biyun ne da Mammynta. 12:30PM driver yadawo da Hanan gida bayan ta yi wulli da takalamanta dakuma jakan makarantan ta a parlour ta dosa kitchen inda taji motsin Mammy. “Mammy I’m home.” Shiru Fannah tayi bata tanka taba “Mammy I said I’m home” nanma shiru. “Mammy I’m sorry.” “Ai ba ruwa na dake Hanan tunda bakiya jin magana kinga in na haifi baby twins d’ina barin sake shiga harkanki ba, saboda su basu gagara in akace musu stop zasu bari not like you.” “Mammy I’m sorry.” “Aini ba ruwa na dake kicigaba da biye wa Daddy, Airah da Aidah (baby twins nata) kawai nasani ina haifansu zamu bar miki gidan nam sekita rashin jinki me kad’an ki.” “Mammy no please karki tafi min da sisters d’ina.” “Toh mesa zan bar miki su? Dan ki koya musu rashin ji suma?” “No Mammy I’m sorry I won’t do it again” ta riqe kunnuwanta. “Are you sure?” “Yes Mammy” “Oya come here” ta wanke hannunta a sink da gudu Hanan tayo kanta Fannah ta d’agata sama “daga yau bara ki sake min b’arna ba?” “Yes Mammy.” “Thats my girl zaki tab’a sisters naki?” Cike da jin dad’i ta gyad’a kai nan Fannah ta ajiye ta sannan ta aza hannunta kan cikinta aikuwa tayi having kick. “Mami najisu Airah da Aidah koh?” Fannah ta gyad’a mata kai. “Mammy se yaushe zasu fito?” “In 3 weeks time in shaa Allah” “Yeyy! Zan zama Ya Hanan koh? Yawwa Mammy zanje wajen Ummimi yin weekends Ya Amal tace zamuyi wasa kuma zata kaini wajen Ya Aiman.” “Wallahi data kyauta min kona samu sakat bari zuwa anjima zan shirya miki akwatinki oya jeki cire uniform naki sauran kuma kice zaki wanke kinji ni ba?” Daidai nan wayan Fannah dake kan counter yasoma ruri ganin Afrah ke kira ta d’aga da wuri. “Mata a gidan Shettima.” “Hehe Mom Hanan maman ‘ya biyu ya jiki?” “Wallahi alhamdulillah ya hidima?” “Se godiya, nikam gown da zansa a bridal shower d’innan nakeso ki rakani store inje in duba anjima.” “Aww ba d’inkawa zakiba?” “Baby yaban enough kud’i siyan na kanti kawai zanyi.” “Toh fa Afran Shettima Allah nuna mana bikin nan naku, zuwa anjima in Amal tazo ta d’au Hanan se in taho muje mu duba miki.” “Yauwa ina wannan meh blue eyes nakin?” “Wai Hanan?” “Eh mana kai! Yarinya ko jaraba?! ai wallahi banson ta sake zuwa mana yin weekends waya na fa ta d’auka ta tsoma cikin miyan kukan Mami, tad’au shampoo tana wanke wa bebinta gashi, farin jallabiyan Baba ta d’auka tana gogawa a k’asa wannan Hanan seku.” “Toh naji karki zagar min ‘ya ahakan Amal keson d’aukanta yau har ina rowa, zanso kema Allah baki ‘ya kaman Hanan.” “Chab! Allah raba I’ve got to go zani booking makeup artist bye!” Ta katse wayar murmushi Fannah ke “su Afrah amarya oh! Wataran kuma na Aiman.” 4:25PM Anas yadawo from office, alokacin har Amal ta tafi da Hanan. Fannah kad’ai ke zaune a parlour tana shan tuwon madara “welcome home Habeebi yau ka k’ariso da kanka barin iya tashi ba.” Murmushi ya sakar mata sannan ya ajiye jakansa ya nufo inda take ya zauna light kiss yamata brushing. “The queen of my princesses I love you.” “I love you too king of my princesses.” “Ina little Fauzi?” “Amal tazo ta d’auketa d’azu wai zatayi weekends achan.” “Flower mesa kika barta haka last weekend ma Hanan batayi a gida ba.” “Toh wake neman ‘yar jaraban chan? Kasan yadda ta buga min ciki kuwa d’azu da safe?” “Ta tab’a mana Airah da Aidah koh?” Ta gyad’a mai kai. “Kinsan Hanan she got no worries se hak’uri we love you much.” “Wallahi nagaji Habeebi daga wannan I’m not getting pregnant again tunda nasamu two in one” “Haba the queen of princesses sauran two bayan wannan.” “In kai zaka haifesu kam ai ba matsala amman bani ba.” Pecking nata yayi a goshi “muje mu wanke miki kan.” “Banaso ai tun jiya nace kamin kak’i.” “Jiya ai nayi wa Hanan ne yi hak’uri Flower” arms nata tayi cycling a wuyansa tare da kissing nasa passionately na ‘yan mintuna “I love you Mr. Fauzi.” “I love you too Mrs. Fauzi tashi muje toh” a hankali ya miqar da ita suka wuce d’aki. ______________________________ *ALHAMDULILLAH!!!* Anan ni MIEMIEBEE na kawo k’arshen wannan littafi nawa me taken *_TANA TARE DA NI_* inda nayi kuskure ko na fad’i ba daidai ba Allah yafemin, kamar yadda kuka sani wannan labari k’irk’ira na ne (fiction) saboda haka adena kwatanta min shi da real life nayi littafin ne dan nishad’i sekuma dan fad’akarwan dake ciki. I will first of al like to thank *you* for reading my novel and supporting me through out, thank you so much as we keep loving each other haters wanda basuda zuciya bayan nace subar karantamin littafi amman sun kasa dan dad’i should keep on hating, mutum in baida maqiya to be kaiba abinda Fans ke cemin kenan kullum, alhamdulillah tunda ina dasu dan haka nake godiya wa haters d’ina keep on hating I got the f*ck finger up for yah! Godiya me tarin yawa ga *Aunty Sis* my sweet mom I love you Allah bar zumunci yacigaba da kare min ke, to *Lubiee (finest)* thank you for your support I’ll love you always like you do ME. To my co writers that have been supporting me through out thank you. Fatima malumfashi Hanefah usman Queen Meemiluv Anee Futha lurv Pherty Lilmeerahcute Munaysat Bebeelo Miss Hafsy Rash kardam Sahaf Miss xoxo Xybab Yusuf Ummi Aysha S.A Azeez Pharty B~B Nafee anker Ummee Adnan Hafsy Rano Xarah B~B Qurratul ayn da sauran wanda sunan su ya kwanta min kusani duk kuna raina. Special thanks to all of my group members *(MIEMIEBEE NOVELS GROUP)* yours support is different I Love you guys so much, Allah cigaba da had’a kawukan mu (OneLove) To my Fans club *(MIEMIEBEE FANS)* thank you for your love and care. From the buttom of my heart nas lisafo duka names na true fans na wannan littafi nawa butbthe prblem is Allah yayi wa wannan littafi masoya dayawa, na rubuta kusan 50 na goge saboda naga fans d’in basu k’arewa kuma banason in rubuta wasu in bar wasu, wai wannan ma wanda nasani kenan ina ga wad’anda bansan su bafah? Thank you so much guys for making my novel talk of the town. *MIEMEIBEE LOVES YOU SO MUCH WOLLAH* akwai lokacinda na fita naje kasuwa wasu ‘yan mata tsaye a gefe na suna hirar Tana Tare Da Ni wata ke cewa Allah had’ata da marubuciyar koda na fad’a musu nice writer’n they couldn’t believe it dan dad’i so dayawa ana bani labarin yadda Fans ke tad’in novel d’ina abinda nakeso kusani shine kamar yadda kukeso na kuke kuma *_TARE DANI_* nima haka nakeson ku nake kuma *_TARE DA KU_* I’m nothing without you guys (fans) kusani comments naku da wanda na gani da wanda ake ban labari akai ke keeping d’ina moving, forward ever backward never in shaa Allah haters will keep on hating till they die munyi gaba bame dawo damu baya. For comments only here’s my digit 07083515399 Allah had’a fuskokinmu agidan Aljannah, AMEEN. BISSALAM!❤ [13:10, 12/18/2016] ‪+234 903 612 6826‬: •° ★°•❣🎀❣🎀 •°•★•°• °•★•° °• •° °•° *TANA TARE DANI...*👫 ❣🎀❣🎀❣ *_written by miemiebee👄_* In dedication to *Aunty Sis💞* 1⃣0⃣0⃣ *SHARHI AKAN* *TANA TARE DANI* 👫🎀❣👫🎀❣ _Assalamu Alaikum_ Da sunan Allah mai rahma mai jin kai Alhamdulillahi Allah ne abun godia da ya nuna mana karshen littafin nan lfy duk da anta samun matsaloli daban daban da korefe korefe na jamaa akan littafin amma Alhamdulillahi Allah mai kowa mai komai ya bata ikon gama shi lfy sbd kyakkyawar niyyata da kuma hakurinta da halayenta nagari tarbiyar kirki data samu wajen iyayenta da kuma masoyanta na gaskia masu nuna mata gaskia suna sakata a kan hanya ta kwarai yasa bata kula duk masu son ganin karshenta ba. _Little advice to d haters_ *Always b urself, express* *urself, have faith in urself, do not go out and look 4 a successfull personality and duplicate it* *TANA TARE DANI*👫🎀❣🎀 Warra luv story..this is really the best luv story of d year Munsha soyayya gashi mun ilmantu mun waazantu kuma yayi mana tsaye a zucia sbd darussan rayuwa da ke ciki. Abinda nake so masu zagin writers su gane shine duk yadda kuka dauki buk en writer a wulakance kuke ganin hauka da jahilci suke yi ku sani yana koya darasin rayuwa komin kankantar darasin kuwa. *Kadan daga cikin darussan MieMie Bae* 1....Soyayya..soyayya wata ginshike ce ta rayuwar aure wadda idan babu ita auren na iya samun tangarda ko barazana da fuskantar matsaloli..soyayyar nan kuma a musulunci ta samo asali tun..hadisai da dama sun bamu labrin yadda Manzon Rahma ya rayu da iyalanshi cikin soyayya,wasu hadisan sun gaya mana yadda yake taya matanshi aikin gd,yake kula dasu yake ji dasu haka kuma yake zaunawa cikinsu suyi soyayya har wanka yake yi tare da matanshi..ya rayu cikin soyayyar matanshi ya kuma koma ma ubangijinmu cikin soyayyarsu. Don haka Annabin rahma shine shugaban masoya na duka duniar nan duk wata soyayya da muke yi yanzu ta samo asali ne a musulunci kuma kwafa mukayi..don ka sumbaci matarka ko ka rungumeta duk sun duk sun samo asali ne a musulunci..wanda kuma har yanzu dabia ce ta larabawa..idan dai har macen nan muharramarka ce. Yanzu ne mutanenmu suka dauka idan kana gwada ma miji soyayya sai ace baka da kunya ko kuma boko tayi maka yawa ko kuma ta cika fitsara..idan kuma marubuciya ce ta gwada yadda ake soyayyar miji da mata a tsaftace don jamaa suyi koyi su kuma gane nuna ma miji soyyaya ba rashin kunya bane sai a fara ce mata yar iska..wlh mata mu farka duk wani abu da marubutan mu ke yi sunayi ne don jan hankali da fadakarwa..mai yasa wasu mazajen sunfi gane ma matan waje? Sbd soyayyar nan da ake masu da kissa da kisisina wadda ta gd ta kasa tsayawa tayi alhalin ta wajen nan babu abinda ta fiki MieMie Bae kinyi namijin kokari wajen nuna muhimmancin soyayya a rayuwar aure sbd ita ke kara so ta kawo shakuwa har aji baa iya rabuwa da juna 2.... Yadda ummimi ta tafi tabar yaranta da mijinta sbd talauci. Wannan wata babbar magana ce da kika tabo wadda a karence karence na ban taba cin karo da irin wannan matsalar ba. Wannan wata matsala ce da take faruwa a arewacin kasarmu kullu yaumun. Mata na zubda yaransu da mazajensu da sunan babu su tafi saudiyya *TUKARU* ko kuma su tafi wani sashe na kasar nan nesa da gd da iyalansu.. tafiya suke basu waiwayen bayansu, sunsa gabansu a hanyar neman dunia kawai suna mantawa da lahira. Duk Wanda kejin waazin malamai da wadanda ke zuwa saudiyya sunsan irin ta'asar da *tukaru* ke tafkawa wasu don rashin tsoron Allah har aure sukeyi kan aure sbd tabar gd da miji da yaya alhalin bai saketa ba kuma haka zata je tayi wani auran don neman abun dunia. Shi arziki da talauci duk na Allah ne..babu mummunan arziki irin wanda aka samu ta hanyar haram wanda kuma neman arziki ta haka ya riga ya zama ruwan dare sai dai muyi fatan Allah ya karemu ya bamu mai albarka..kuma irinsu Ummimi a banza suke karewa dangin a wofi daga baya sbd dama duk wanda yahau motar kwadayi tashar wulaknci zata aje shi. Ga uwa uba alhakin iyaye,yaya da kuma miji.chaiiiii gaskia zunubin yayi yawa. Nasu hali irin na Ummimi gareku Mie mie Bae ta gwada maku illar haka takuma ce don Allah a gyara. 3...Illar rashin uwa ( ba ina nufin wadda Allah yayi ma waadi ba) ina magana ne kan wadda ta tafi tabar yayanta da dacinta rashin rashinta wanda hotonta na rashin kirkinta baya taba goguwa a zukatan yayanta ..watakan rashin uwa ta irin hanyar nan ba Karamin illa da gibi yake ma rayuwar yara ba sbd basu manta abinda tayi masu wanda hakan kesa wasu su tashi cikin kunshi da bakin ciki su kuma tsani mata sannan wasunsu su fada harkar shaye shayen nan na zamani har su koma suna aikin Assha irinsu sata da raping..jst like how Anas raped fannah @ deir young age..ai sun samu abokan gaske ko kuma jajirtattar mata Kamar fannah sannan zaka ga suna rage wasu abubuwan a hankali har su daina ma gaba daya jst like Anas 4....Tasirin gyara musamman daga wajen wanda kake so ka yadda dashi kuma kake kaunarshi Miemie na yaba maki sosai ta wannan fannin Gyara ko a musulunci baa yinshi da cin fuska ko cikin bainar jamaa.. Idan dai har tsakaninka da Allah gyara kake son yi ma mutum to kayi shi ta hanyar da addini ya koya mana..ta hanyar lallashi nasiha da ban baki Kamar yadda Fannah tayi amfani da wadan nan makaman wajen gyara gurbatacciyar rayuwar Anas a hankali.. Tayi amfani da ilminta da matsayinta na ya mace da aka sani da iya kissa ta gyara *Anas* a hankali tana mai addua kuma har Allah ya nuna mata lokacin da ya shiryu ya dena masifa, fushi, zuciya, shaye shaye,yaudarar yan mata da sauran munanan halayen data gyara mai ta hanyar da addini ya shimfida Haka kuma duk wanda ke gyara sai yayi hakuri Kamar yadda *Fannah* tayi sbd banna ce ke faruwa lokaci daya amma gyara sai a hankali. 5....Amfani da fa'idar hakuri Kamar yadda *Fannah* ta yafe ma *Anas* duk da zunubinshi mai yawa ne amma daya tuba kuma tasan yayi nadamar gaskia Haka ake son musulmi kwarai ya kasance mai yafiya..kuma yadda yaran ummimi suka yafe mata haka ake so duk wanda yace yasan yayi laifi amma yayi nadama kayi hakuri ka yafe mai to don Allah mu daure mu dinga yafe ma junanmu sbd ita kanta duniar da abinda ke cikinta kalilan ne kuma ita duniar nan ba matabbata bace MieMie Bae kinyi kokari da kika tabo mana illar raping ko kuma ince illar Aiken yara mata kananu da daddare koma da ranan ne musamman idan kasan cewa unguwarku is not secured..Yanzu Allah ya kawomu wani zamani damu iyaye mata ke sake kana tarbiyar yaranmu mata musaman masu karancin shekaru.. Duk wanda ke aiki police station ko asibiti yasan yadda rape case ya zama vry rampant kuma duk sbd sakaci da saken da muke da yayanmu hannun almajirai,masu gadi, yaran unguwa,uncles, cuz,nephew duk babu yadda bata kasancewa..ya kamata musa ido mu gyara Kamar yadda MieMie Bae ta gwada mana illar hakan da irin rayuwar matsin da hakan ke jefa victim and her parent.. Kuma wani tabo ne da baya kankaruwa har abadaaaaa Ina tsaya haka nan sbd lessons din cikin tana tare dani basu taba karewa sai dai inbar sauran masoya su fadi nasu suma. Tunda ni uwace bai kamata in hada komai in cinye ba. Zanyi amfani da damar nan don mika godia ta ga Yan grp dinmu na novel *NOVEL 3* *Fateemah Musa* *Fateemah Dan maliki* *Zareenah* Kunfi kowa son *Tana Tare Dani* MieMie Bae na sonku,nima ina sonku muna kuma *tare daku* *ALLAH NA TARE DA KE* # _Babbar tarayya_ *INA TARE DA KE* # _Mumcynki_ *SUNA NA TARE DA KE* # _Your true fans_ _Har abada insha Allahu_ *Aunty Sis* 💞 Nason dukkan *MieMie Bae's fans* a duk inda kuke kuma *INA TARE DAKU* *Ina rokon Allah ubangiji* *ya cigaba da daukaki yasa kifi* *haka,ya kara maki basira da hazaka,ya kareki daga* *sharrin makiya da mahassada na fili dana* *boye ,da yan black belly da masu kambun baka* *Allah ubangiji yayi ma rayuwarki albarka yasa ki fara karatunki lfy ki gama lfy ya kareki daga sharrin azzaluman malamai da kadangarun campus* *Idan lokacin aurenki yayi Allah ya* *azurtaki da miji nagari* *wanda zakuyi zama har a aljannah firdaus* _Dx All wat ur mum wl say_ *I luv u so much*💞❣🎀 💞 *Aunty Sis*💞