[8/19, 17:55] Mom mashkur & Afrah: *UNGOZOMA* (Mai karɓar haihuwa) NA MAMAN AFRAH GARGAƊI⚠️ Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ta kowace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowace kafa ba sai da izinina a kiyaye. Page 1️⃣➡️2️⃣ Dare ya tsala, ko ina tsit kake ji babu abin da yake tashi sai kukan tsintsaye da karnuka. A can cikin ɗakin Gwaggo Ramma ita ce kwance a kan gadonta na kara irin na mutanan da ɗin nan tana shirgar bacci sai ƙaran munsharinta da ke tashi a ɗakin tamkar an shaƙewa zakara wuya. Mai Gari ma da yake can yashe a kan tabarmar kaba yana sharar nasa baccin ya ɗaga kan nan nashi sama baki a buɗe sai sakin munsharin yake a gefe ɗaya yana sakin tusa a kai -a kai saboda alalar da suka ci da rana sannan ita suka ƙara ci kafin su kwanta. Juyi Mai Gari ya yi a cikin baccinsa ya ji wani uban wari da ya durfafi hancinsa hannunsa ya kai ya buɗe mayafin da ya rufa da shi sabo da sanyin da ake zugawa, jim kaɗan cikinsa da ya kumbura ya shiga ƙara ƙulululuuuu bakam ya tashi a 360 ya yi jifa da abin rufar sai gashi a zaune hajaran majaran yana jefa idanu a cikin duhun ɗakin warin da ya haɗe ɗakin ya sanya shi sanya hannu biyu ya toshe hancinsa. Ƙaran tusar Gwaggo Ramma da ta saki guda biyu a jere su ne suka daki kunnuwansa a take cikin Mai Gari ya cigaba da hautsina wa. "Kayyasa! Bar ganin ka tara ka kiyayi mai nema, taɓɗi sinasir wannan tusa da kike yi Ramma kamar an rufe mutum a ɗakin mushe duk kin haɗe ɗaki da wari" Cewar Mai Gari a fili yana ƙara danna hannayensa a hancinsa jin warin tusar tasu gabaɗaya ya haɗe ɗakin. Hannu ya kai ya sakarwa Gwaggo Ramma wani ɗaɗe a ƙwabrin ƙafarta a kiɗime ta tashi ta zaune mazaunanta sai kuwa ƙaran wata tusar ya fito darrrrrr. "Subhanallahi! Ni Ramma a cikin masai (Toilet) Nake ko a ina? "Ta furta a fili jin warin ɗakin ya game ko ina. "Babu wata masai a cikin ɗakin ki kike haba! Ina dalili duk kin kumbura mini ciki tun da na tashi da ƙaran fitar iskar mazaunanki na fara cin karo tamkar ana sace iskar tayar motar tifa duk kin hargitsa mini cikina... Kafin Mai Gari ya ƙarasa maganar da yake yi fitowar wata ƙatuwar tusa mai cike da mugun ƙara ta masa shamaki da sauran maganar da yake son faɗa, da kallo mai kamar harara da kuma ka raina mini hankali Gwaggo Ramma da ta kunna tocilan ta bi Mai Gari dan sai yanzu ta tabbatar da cewa ashe dai ba ita kaɗai ta cika ɗaki da wari ba har da shi. Kunya ce ta sanya Mai Gari ya ɗauke kai dan a halin da ake ciki ma yanzu wata tusar ce take son fito masa amma yana ta yaƙi da ita a kan kar ta suɓuce ta fito dan haka sai ya shiga murtsika mazaunansa a kan tabarmar kabar da yake zaune wacce ko arziƙin shimfiɗa bata samu ba. Amma cikin rashin sa'a duk ƙoƙarinsa na ganin ya danne tusar nan haka ta ringa ɓarin mahaukaciya da ƙoƙarin nasa har dai ta samu nasarar fitowa tare da bada wani sauti da ya sanya Gwaggo miƙewa tsayi ba tare da ta san hakan ko ta shiryawa hakan ba dan ita dama a tsorace take da gidan nan da suka tare a jiya, wanda taku kaɗan za ka yi daga gidan ka je katangar maƙabarta da yake ma katangar ba wani tsayi ne da ita ba idan kana daga tsaye kana iya hango kaburbura, wannan dalilin ne ya sanya ƙaran fitowar tusar Mai Gari hautsila ƴan hanjin cikin Gwaggo Ramma. A take cikin nata ya wani birkita sai ita ma ta saki tusar ɓet-ɓaɓet, lokaci guda ta ji wata gudawa ta matso ta. "Na shiga uku ni Ramma, in banda abin majinyaci na mai magani ne, yanzu a cikin daren nan anya kuwa zan iya zuwa bayi, in sauke nauyin cikin nan nawa, gashi kuma gudawa bata da haƙuri ko misƙala zarratan idan ta taho dole ne sai mutum ya tsiyayar da ita sannan zai samu salama... Kafin ta dire maganar da take yi a zuciyar ta Mai Gari ya zabura ya miƙe tsaye a can gefen tabarmar da ya kwanta ya hangi tashi tocilan ɗin dan haka bai yi ƙasa a gwiwa ba ya kai hannu ya ɗauka da sauri ya juya ba tare da ya bi ta kan Gwaggon ba ya nufi hanyar fita daga ɗakin dan shi a yadda yanzun nan gudawar ta matso shi ba ya jin ko minti biyu zai iya jurewa ba tare da ya yi kashi ba dan haka ya ɗaura aniyar ficewa ya riga matarsa shiga bayi sabo da ya san kaf gidan dai bayi ɗaya ne kuma ya san matsawar Gwaggo ta riga shi shiga bayin nan sai ta Allah dan ya san zai iya sakin kashin na a wando kuma abon kunya ne a ce shi Mai Garin GUMURZU ya yi kashi a wandonsa. Gwaggo kallon Mai Gari ya suri fitilarsa ya nufi ƙofar fita sai zuciyarta ta raya mata cewar shi ma kashin zai je, dan ta san a yadda yake da tsoro kamar farar kura babu abin da zai fitar da shi daga ɗakin a daren nan sai dai kashi, dan ta ji yana tusa kuma ta tabbatar bayi zai yi wa dirar mikiya, wanda hakan kuma tamkar yaƙi zai yi da rashin fitowar nata gudawar wani kallo ta yi wa bayan koɗaɗɗiyar rigar sanyin jikinsa kafin cikin azama ta yi taku biyu ta rafko ƙasan rigarsa, Mai Gari jin an riƙe masa rigarsa sai da ya ji tamkar ya saki ihu dan ya ji kashinsa daf yake da fitowa gashi Ramma za ta masa cikas ɗin fitowar kashin a kan lokaci. "Wallahi in dai bayi za ka shiga sai dai ka jira har in shiga in fito dan kashina yana bakin boda daf yake da hantsilowa babu abin da ya fi kamata da kashin nawa sai dai ya ji shi a cikin duniyar masai(Toilet) " Cewar Gwaggo Ramma cikin sababi. Mai Gari ji ya yi bashi da ƙarfin yin magana dan yana buɗe bakinsa gani yake kashin ne zai zubo dan haka a hankali ya juyo ya fuskanci Gwaggo Ramma ya ɗaga hannu biyu ya fara mata maganar bebaye dan ba ya so ya buɗe bakinsa gudawar ta fito bai shirya ba.Wata uwar harara Gwaggon ta jefa masa ta ja rigarsa ta mayar da shi gefe guda dan bata jin tana da ishashshen lokacin da har za ta tsaya kallon zancen bebayansa bare har ta gane mai yake so ya faɗa mata. "Kar ki mini haka Ramma" Cewar Mai Gari cikin raɗa-raɗa dan ba ya so ya buɗe baki sosai kashin ya zubo. Ai kuwa cikin rashin sa'a maganar da ya yi duk da ya yi ta ne cikin raɗa amma sai dai kashin nan ya yi masa barazanar fitowa, da sauri ya saki fitilar hannunsa ya kai hannu biyun ya dafe mazaunansa saitin mafitar kashin dan yana ganin hakan shi kaɗai ne salama a gare shi na hana fitowar kashin ba shiri. Gwaggo kuwa ko ta kan Mai Gari bata bi ba, ta buɗe ƙofar bakam ta fice a sukwane tana fatan Allah sa dai ta kai har bayin ba tare da gudawar ta zubo ba bare har ta ɓata zaninta, takalmin ma ƙafa ɗaya ta saka ɗayar kuma bata samu damar sakawa ba tsabar yadda kashin ya matse ta a hannu ta ɗauki ƙafa ɗayar takalmin. Cikin gudu-gudu sauri-sauri ta tasamma hanyar da za ta sada ta da bayi da yake da ɗan tazara daga ɗaki zuwa bayi. Salele da shi ma kumburin cikinsa ne ya tashe sa yadda lokaci guda ya ji gudawa tana neman hanyar fitowa bai yi wata-wata ba ya kunna fitilar wayarsa mai madannai ya buɗe ƙofa ya fito burinsa kawai ya gan shi a cikin bayi, yana fitowa ya saka takalmansa a baibai da gudu ya tafi sai da suka kusan cin karo da Gwaggo da ke nata saurin mai haɗe da gudu tana riƙe da ƙafar takalmi a hannu da kuma fitila, ganin ita ma ta doshi hanyar bayi mamaki ya rufe shi, kafin ya dawo daga mamakin ya hango Kakansa Mai Gari shi ma ya taho da gudu hannayensa dafe da mazaunansa shi ko arziƙin saka takalmin ma bai samu ba. "Bala'i yau ake yinta wallahi sai dai ku hau layi bayana dan babu wanda zan ɗaga wa ƙafa ya shiga bayin nan sai na shiga" Cewar Salele a zuciyarsa yana ƙara ɗaga ƙafa ganin Gwaggo da gaske neman rigaye shi zuwa take yi. Gwaggo da har wani numfashin gajiya take saukewa sai dai ganin ta kusa ƙurewa hanyar bayin gudu sai kawai ta ɗan ji daɗi a ranta, amma kuma tana dab da ƙofar bayin kawai sai ganin Salele ta yi kamar wanda ya diro daga sama ya shiga gabanta zai shige cikin bayin. Wani irin zaro idanu ta yi tare da buɗe baki ta shiga cewa. "Salele ka yi uwarka da ubanka da muka kawo su duniya, kai kuma suka kawo ka duniya kar ka shiga bayin nan wallahi idan ka shige ka shiga haƙƙina kai hatta da alhakina wallahi ka ɗauka dan ko ƙafar takalmi ɗaya ban samu zarafin tsayawa saka wa ba duk dan in je in sauke nauyin cikin nan nawa... Kafin ta kai ƙarshen maganar Salele da ko kallo bata ishe shi ba, burinsa ya je ya tsugunna, haka ya shige ya barta a bakin ƙofar, dan duk saurinta ya riga ta ƙarasawa. A hankali ta ɗago ƙafafunta ta baro bakin ƙofar sabo da wani wari da ya far wa hancinta, ga ƙaran gudawar Salele hakan ya tabbatar mata kashin ta yana dab da zubowa. Jin hakan sai ta haɗe ƙafafunta ta matse su ta ɗan sunkuya duk dan yaƙi da gudawar kar ta fito. Mai Gari da shi tsabar ruɗewarsa bai hangi Salele ba ma yana ƙarasowa ganin Gwaggo a sunkuye sai ya ji ransa fari ƙal dan haka ya nufi ƙofar bayin gadan-gadan. Yana shirin afkawa sai ya jiyo nishi da ƙaran kashin Salele tamkar mace mai nakuda. "Oh ni Mai Gari Garba ma ga larura auren namiji da ƴaƴa, yanzu a ce wai kashi ma in za ka yi sai kana jiran layi sai ka ce wanda kake zaune a gidan haya" Ya faɗa a zuciyarsa yana jin babu daɗi a ransa da ya baro gidansa ya dawo wannan gidan sabo da aljannu da suke tsorata shi ashe dai ya yi gudun gara ne ya tarar da zago. Gwaggo kuwa waige-waige ta fara ai kuwa ta sauke idanunta a kan wani tsohon kwanon silba rafkeke tana daga sunkuyen ta fara takawa a duƙe har ta kai wajen kwanon ta ɗauka dan ita da ta yi gudawar nan a zanenta gwara ta yi a kwanon dan ta san Salele ko kusa ba zai fito yanzu ba. Tana ɗaukan kwanon sai ta nufi wajen wani tsohon langa-langa za ta laɓe a wajen ta juye abin da yake cikinta, Mai Gari ma ganin ta ɗauki kwanon ta cikin hasken farin wata idanunsa suka sauka a kan wata tsohuwar samira (Kwano) Yashe a wajen dan haka shi ma bai yi bori da sanyin jiki ba ya ɗauke hannayensa daga jikin mazaunansa dan yana ganin nesa ta zo kusa, da sauri ya ɗauki kwanon ya shiga wani ɗan lungu da yake kusa da bayin. Gwaggo Ramma da Mai Gari kusan a tare suka yi masauki a kan kwanukan da za su juyi abin da ke nuƙurƙusar su, amma kuma mai? Ƙaran wani uban bugu da aka yi wa ƙofar gidan nasu ne ya saka Gwaggo miƙe wa tsaye babu shiri, a ɓangaren Mai Gari ma hakan ce ta kasance dan shi bai san lokacin da ya faɗi ba daga shi har kwanon da ko ɗigon kashi bai yi a ciki ba, da sauri ya daure ya tashi dan ya san babu mai ɗaga shi ko taimaka masa ya tashi. Salele kuwa da shi ma bai kai ga gama nashi kashin ba hannunsa yana karkarwa ya ɗauki butar da take cikin bayin ya wanke ya miƙe daga tsugunnon, ko ta kan wayarsa raka ni kashi da ta faɗi a bayin bai bi ba, haka ya fito da gudu daga bayin. Yana fitowa Mai Gari ma ya shawo kwanar lungun da ya shiga ai kuwa suka ci karo goshin su ya bugu da na juna, Gwaggo Ramma da take saurin ɗaura zanenta amma ya ƙi ɗauruwa sai kawai ta riƙe zanen a hannu fitilarta kuwa a baki ta saka a take ta ranta a na kare dan babu batun yin gudawa tun da ga abin da ya fi gudawa ya tunkaro su. Mai Gari kuwa ko ta kan goshinsa bai bi ba da suka yi karo da jikan nasa a haka ya fara gudun ceton ransa yana riƙe da tazuge da hannu ɗaya, ɗaya hannun kuwa yana hantsar wandonsa dan kar wandon ya faɗi. "Ya Rahmanu, ya Rahimu" Su ne kalmomin da suke safa da marwa a zuciyar Mai Gari, dan ya san yau sai ta Allah ɓarawo a hannun mata tun da dai fatallun da ake labari a garin GUMURZU ta kawo musu farmaki sai yadda hali ya yi dan ya san shikenan kuma za ta musu ɗauki ɗai-ɗai shi da matarsa da kuma jikansa. Salele da yake rike da tsantsar wandonsa da hannu biyu dan shi ma bai sami zarafin ɗaure tazugen na shi ba, a haka ya durfafi ɗakinsa yana fatan ya shige ya kulle ba tare da fatallun ta buɗe ƙofar gidan ta shigo ta fara ta kansa ba dan yanzu bugu bibbiyu ake yi wa ƙofar langa-langan gidan tamkar za a ɓalle, har ma da jikin langa-langan wanda aka kewaye gidan da shiw. Yana shiga ɗakin na shi ya banka ƙofar tare da garƙama sakata, jingina ya yi a jikin ƙofar yana mayar da lumfashi. Jin bugun ya yi yawa ya yanke shawarar ya lallaɓa wa ya koma makwancinsa ya kwanta sai ya rufa in ya so sai yake karanta fatiha da salatin annabi S.A.W ne ko da a ce fatallun ta zo in za ta ɗauke shi sai ya mutu da ɓurɓushin imani tun da yana karatu ba wai waƙa yake yi ba. Yana ɗaga ƙafarsa ya sauke ta a kan kwalbar lemon kwalbar coca colan da ya sha kafin ya kwanta ai kwa ta tafi suuuuuu tare da shi tamkar wanda yake a kan sirnane sufar da ya yi sai ya je a kife bakinsa ya bugu da simintin ɗakin da ko ledar tsakar ɗaki bai samu ba. A hankali cikin zafin ciwo na goshinsa da suka yi gware da Mai Gari da kuma zafin buguwar da bakinsa ya yi amma a haka ya lallaɓa ya hau kan kalalliyar katifarsa ya kwanta lifet tare da rufa gabaɗaya har kansa sai ya ji ya gagara karanto komai ma sai faɗuwar da gabansa yake yi dan ƙirjinsa sai dakan lugude yake yi tamkar Bafulatana ta samu surfen hatsi(Gero). Gwaggo Ramma kuwa riƙe da zanenta ta shiga ɗaki, tana zazzare ido dan ta daina jin kashin ma kwata -kwata tana shiga ta saka sakatar sama da ta ƙasa. Daɓas ta zauna tana mayar da numfashi, a cikin duhun ɗakin dan fitilar tata ma ta faɗi a hanya. "Kai wallahi kam ni dai ina ganin takaici, haka kurum an ɗakko mu an kawo mu ƙarshen gari kusa da maƙabarta sunan ina matar Mai Gari gashi yanzu jafa'i zai same mu da rana tsaka fatallun da aka ce tana kashe mutane mus har lahira ga shi ta zo za ta yi wa gidan da muke ciki kutse da tsakar daren nan... Ƙaran bugun ƙofar ɗakin nata ne ya sanya ta haɗiye wani yawu muƙut. A take ta shiga kokawa da lumfashin ta zuciyarta ta shiga raya mata cewa fatallun ba guda ɗaya bace wata ce take buga ƙofa wata kuma tuni ta shigo ta saman iska... Maman Afrah Whatsapp 09013181851 *META FORCE ARZIƘI DAGA ALLAH* ƳAR UWA SHIN BAKI DA LABARIN META FORCE? DA IRIN ƊINBIM ARZIƘIN DA AKE KWASHEWA A CIKINSA, YA AKA YI BAKI YI REGISTER BA? KO BAKI DA BUƘATAR KUƊAƊEN DA ZA KI YI HIDIMAR YAU DA KULLUM? TO KI ZO NI MAMAN AFRAH NA ZO MIKI DA HANYAR SAMUN KUƊI TA WAYAR HANNUNKI KUƊIN YIN REGISTER KAWAI ZA KI TANADA 9K DUBU TARA DOMIN ANA YIN REGISTER DA DALA 5 NE SAI DAI ALLAH KAƊAI YA SAN IRIN RIBAR DA ZA KI SAMU DA KUMA ALKAIRAN DA YAKE CIKIN KASUWANCIN. IDAN KINA SO SHIGA KUMA DA GASKE KIKE KI MINI MAGANA A WANNAN NUMBER 09013181851 IDAN BA YI ZA KI YI BA KAR KI MINI MAGANA DAN BANA SON ƁATA LOKACI! [8/19, 17:57] Mom mashkur & Afrah: *UNGOZOMA* (Mai karɓar haihuwa) NA MAMAN AFRAH F.C.W GARGAƊI⚠️ Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ta kowace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowace kafa ba sai da izinina a kiyaye. Page 3️⃣➡️4️⃣ Gwaggo Ramma sosai jikinta ya shiga karkarwa jin ana ta buga ɗakin nata, a take ta fara da na sanin rufe ɗakin ita kaɗai da ta san haka za ta faru ai da ta jira zuwan Mai Gari mijinta in ya so ko ma mene ne zai same ta sai ya same su tare, musamman ma da ya kasance Mai Garin ba shi da ɗakin kansa a gidan tun da jiya ne suka tare a gidan kuma ɗakuna biyu ne kaɗai a gidan suka ɗauki ɗaya Salele ya ɗauki ɗaya. "Ni Ramma na shigenge yanzu haka Mai Gari ɗakin Salele suka shige ni ina nan ni kaɗai kamar mayya, an bar ni a gefe kamar yajin ƙosai, haka fatallun nan za ta zo ta yi awon gaba da ni, ba tabbas abin da yawa mutuwa ta shiga kasuwa" Ta faɗa tana sharar ƙwallar tausayin kanta. Mai Gari kuwa da yake faman buga mata ƙofar yana jira ta buɗe masa ya shiga, sai dai tsoro ne fal ransa dan haka ma ya ƙi yin magana sabo da gudun kar fatallun ta jiyo maganarsa ta ji daɗin tsallakowa ta sama dan haka himma kawai ya bada wajen bugawa dan ya samu ta buɗe masa shi ma ya afka ɗakin. "Yau kam na ƙara yarda da kirarin, ƊAKI KO KANA ZUBA KA FI WAJE" Mai Gari ya faɗa a ransa yana cije leɓe ganin ya ɗaki amma yana waje sanyi yana ƙarewa a kansa ga tsoron fatallu. Jin har lokacin ba a buɗe masa ba kuma dai fatallun da alama ba fasa buga ƙofar za ta yi ba dan zuwa yanzu tamkar za a ɓalle ƙofar kai har ma da langa-langan da aka yi wa gidan ƙawanya da shi wannan ne babban abin da yake ƙara kaɗa hantar gabaɗayan waɗan da suke cikin gidan, hakan ne ya sanya Mai Gari hasaso cewa dab yake da kai wa barzahu ziyara matsawar dai fatallun ta ɓalle ta shigo gidan domin shi kaɗai ne a tsakar gida kowa ya shige ɗaki ya banke a hankali ya fara bin bango tamkar wani ƙadangare, har sai da ya dangana da saitin inda windown ɗakin yake, cikin karkarwa jiki da bugun zuciya ya fara dafa bangon a hankali dan ba ya fatan ko motsinsa a jiyo bare a kawo masa farmaki, hatta da numfashi ɗai-ɗai yake yi idan ya shaƙi ɗaya sai ya ɗan jima zai huro sai ya sake shaƙa duk dan sabo da tsaro ba wai dan tsoro. Bayansa ya waiwaya sai kawai idanunsa suka masa gizo da ganin wata mata da farin kaya a take cikinsa ya ɗuri ruwa maƙoshinsa ya bushe ƙamas cikin hanzari ya kama katangar ya ɗare windown ƙofa uku ce a windown amma ƙanana Mai Gari cikin ruɗani ya dage ya tura kansa cikin ƙofa ɗaya, ta cikin hasken da ya ratsa ɗakin ta windown ya hangi Gwaggo da ta yi zaman ƴan bori a ƙasa sai wani abu take kamar zararriya "Taɓ! Lallai duniya gidan kashe ahu, yanzu Ramma ce a cikin wannan halin lallai abin al'ajabi ango ya kwana da ƙunzugu" Cewar Mai Gari a zuciyarsa amma halin da yake ciki ya hana shi yin ko da murmushi ne bare a kai ga dariya. Ƙoƙarin yaƙi da harshensa yake kafin a kai ga laɓɓa domin ya ba shi damar furta wata kalma da za ta ankarar da Ramma cewar yana window yana jiran ta kawo masa ɗauki amma ganin fitowar furuci daga bakinsa zai ƙara kabbama halin tsoron da yake ciki sai ya ƙara jan bakinsa ya tamke shi gam. Cikin rashin kuzari ya ɗaga hannunsa guda ɗaya ya ɗan daki jikin bangon ɗakin daga ciki amma kuma Gwaggo tana jin sautin taɓa bangon sai hakan ya ƙara rura wutar tsoro da fargabar da take ciki a nan take cikin ta ya karta sai sautin tusar ta kawai kake ji ƙuiittt-ƙuiit tamkar sabuwar bodara. "La sharikalahu Allahu, la sharika lahu Allah, manzallazi yashfa'u indahu illah bi'izinihi" Gwaggo ta faɗa a ranta tana jin tamkar ƙasa ta tsage ta shige ciki ko ta samu sukuni. "Mai Gari ne mijinki daure ki lallaɓo ki buɗe mini in samu ni ma in shigo daga... Ƙaran buɗewar ƙofar gidan ne da ya ziyarci majiyar sautin Mai Gari ya dakatar da shi daga ƴar maganar da ya samu kuɓutowar ta daga bakinsa da ya bushe wanda ya yi ta a cikin salon raɗa-raɗa tamkar wanda mura ta yi wa kamun kazar kuku. Dan ita Gwaggo a halin da take ciki ma bata tsinkayi muryar mijin nata ba ma bare har ta san abin da ya ce hasali ma bata san ana yi ba wai kunu a maƙota ita abu ɗaya kaɗai ta san tana iya jin sa a kunnuwanta shi ne sautin fitar tusar ta sai kuma bugun ƙofar gida da kuma langa-langan gidan, hana rantsuwa ta ji bugun jikin bango wanda ta yi amanna da cewa fatallun ce ta tsaga bango za ta shigo ɗakin hakan kuwa shi ne ya ƙara kaɗa mata hantar cikinta bare kuma a yanzu da ƙaran buɗuwar ƙofar gidan ya sanya ta ƙara saka wa a ranta cewar suna daf da zama gawarwakin da za a kai maƙabartar da take kusa da su a wayewar garin gobe. Cikin sanɗar rarrafe ta fara rarrafawa domin ganin ta sama wa kanta mafaka a cikin ɗakin ko Allah zai sa ta tsira da ranta, haka ta fara rarrafe riƙe da zanenta a hannun ta wanda har yanzu bata samu zarafin ɗaura shi a ƙugunta ba, tana fara rarrafen ta ji gabaɗaya gwiwoyinta sun sage hakan ya tabbtar mata da gwiwar ba za ta iya ɗaukanta ba, babu shiri sai ta mayar da akalar rarrafen nata ga jan mazaunanta, amma kuma tana ja sau biyu sai ta ji tamkar tana janyo gudawar da ta samu komawar ta ne dan haka ta yi rufda ciki ta fara jan cikin ta a haka ta kai wa wani duro irin gajeran duro ɗin nan marar tsayi cikin ƙarfin hali ta lallaɓa ta yi dabara ta ɗaura zanen nata sai ta shige cikin duron da aka zuba dawa wacce ko casawa ba a yi ba sai kuma cikin sanɗa ta ɗauki wata fantekar kukar kaɗi ta kifa a kan nata ba tare da damuwa da yadda gabaɗaya ta sheƙawa jikinta kukar ba amma a haka ta duƙunƙuna a cikin duron tana danne atishawar da take son fitowa sabo da kukar da ta shaƙa, amma bata damu ba fatan ta wurin ya zama maɓoyarta da fatallun ba za ta ganta ba. Mai Gari kuwa tun da ƙofar nan ya ji ƙaran buɗewar ta sai da ya ƙara ƙanƙame ƙarfen windown sabo da gudun faɗowa dan ya lura karkarwar da jikinsa ya ɗauka kamar mazari ko kuma mai masassara dan ya san ko da a ce fatallun za ta kashe kowa to ya yi imani ta kansa za ta fara tun da shi ne a tantagayyar tsakar gidan bai samu damar afkawa ɗaki ba. Ganin Gwaggo ta fara ƙoƙarin sama wa kanta mafaka sai ya shiga gyaɗa kai kamar wani ƙadangare wai hakan alamu ne yake yi wa Gwaggo da bata san da wanzuwarsa a wajen ba, dan ta taimaka masa amma ina! Gwaggo ta samu nasarar shigewa cikin duro mai dawa ta ƙara da sheƙawa kanta kukar kaɗi da kifa wa kan nata fanteka dan tana ganin ta samu maɓoya. Abin duniya ne ya haɗe wa Mai Gari goma da ashirin jin ƙaran tahowar mutum da alama dai fatallun ta samu nasarar shigowa cikin gidan, Mai Gari cikin ficewar hayyaci ya fara ƙara kutsa kansa cikin ƙofar dan ya samu gangan jikinsa ya shige ko ya dira cikin ɗakin amma ina! Sai ya ji hatta da kafaɗarsa ba za ta shige ba bare a yi zancen shigewar gangan jiki. Wani fitsari da ya taru ya samu mafaka mararsa ne ya samu nasarar fitowar shaaaa kamar an buɗe famfo sabo da tsabar duniyar tsoron da ya tsinci kansa a ciki cikin sauri ya saki inda ya kama sai ya zamana ya riƙe da hannu ɗaya, hannun ɗaya ya miƙa ya shafo mazaunansa ai kuwa zaton da yake ya zama gaskiya domin kuwa jin hannunsa ya sauka a kan asalin fatar jikinsa ba wai wando ba hakan ya sanya ya tuna ashe dai tun lokacin da ya taho bai ɗaure mazugin wandon ba, da ya tashi hawa windown ya ma manta da cewa wandonsa ba a ɗaure yake ba. "Kai ni na ga abin da ya ture wa buzu ɗani, yau mazaunan Mai Gari ne a buɗe muraran babu rufa sai ka ce mazaunan ɗan akuya" Mai Gari ya faɗa a ransa yana fashewa da wani irin kuka marar sautin sai hangame baki yake yana jin ina ma yana da layar zana da ya ɓace ɓat ya huta da wannan tashin hankalin da yake ciki. A ɓangaren Salele ma tun da ya ji ƙaran buɗewar ƙofar sai lumfashinsa ya tsaya cak, dan shi babu abin da ya ƙi jini sama da fatallun nan da yake ta ji ana labarin ta a gari amma sai ga shi yau ta shigo musu gida tabbas ya san suna cikin jalala. Jin yana neman mutuwa sabo da rashin numfashi da ƙarfi ya huro numfashin tare da buɗe rufar da ya yi domin ya shaƙi iska da kyau. Malam Mammani wanda shi ne ya yake ta bugun ƙofar gidan har dai ya samu ƙofar ta buɗe da kanta shi ne ya shigo cikin gidan na Mai Gari a rikice dan shi ma a tsorace yake sabo da gamo da ya yi a hanyar zuwansa gidan na Mai Gari domin shi ma matarsa ce take naƙuda wannan ne dalilin da ya sanya ya fito domin zuwa ya kira INGOZOMA Gwaggo Ramma dan ta ƙarɓi haihuwar sabo da duk garin Gumurzu ita kaɗai ce take karɓar haihuwa. Da yake a tsorace yake wannan dalilin ne ya sanya yake yi wa gidan bugun ta ko ina sannan yanzu ma da ta shigo gidan ko sukunin yin sallama bai samu ba burinsa kawai ya samu mafaka, tun da ya san masu gidan suna can suna bacci tun da ba su suka buɗe masa ba tamkar zararre haka ya shiga baza idanu cikin wani irin faɗuwar gaba ya zaro idanunsa domin tabbatar da abin da idanun nasa suka yi arba da shi wato mutum ya hanga a maƙale a jikin bango daga wajen window yana sukur-sukurtu ji ya yi tamkar ya juya ya koma inda ya fito sai dai ba zai iya ba sabo da tsoron fita yake. Cikin wulga ido kamar tsohon munafuki ya fara neman mafakar fakewa. Ta cikin farin watan idanunsa suka sauka a kan dabbobi, inda runfar su take suna ɗaɗɗaure sai dai dukan su a kwance suke babu wani dogon tunani Malam Mammani ya nufi turken dabobin nan. Amma jin ƙaran ƙofar da ya biyo ta can sai ƙafafunsa suka sage masa ƙafafun nasa suka gagari ɗaukan gangar jikinsa dan yanzu ya gane fatallun ma ashe sun cika gari ne tun da ya baro wata da ta biyo shi a can baya sannan yanzu shigowarsa ya hangi wata maƙale a window dan haka sai ya zube a ƙasa cikin ƙarfin hali ya shiga rarrafawa ya nufi turken dabobin yana zuwa dabobin ganin an tunkaro su sai suka fara tashi tsaye kowanne ya wage baki yana meeeyyyyy. "Ku yi haƙuri dabbobi kun samu baƙon bil adama a cikin talatainin daren nan, ku yi shiru in samu in yi ɓadda kama a cikin jinsinku sabo da kar fatallu ta yi arba da ni in shiga tara ba ma uku ba" Cewar Malam Mammani a hankali cikin raɗa-raɗa kamar wanda yake magana da mutum mai hankali yana kutsawa cikin ayarin dabbobin wanda suka cigaba da raira kukan su tamkar dai an zuga su ne an ce su yi ta yin kukan babu ƙaƙƙautawa. Sai da ya shige tsakiyar su duk da warin kashi da zarnin fitsarinsu amma ta haka ya shiga har sai da ya je kusa da wani jigo wanda ba a ɗaure dabba a yana zuwa bai jira komai ba ya kama igiyar jiki ya sarƙafa hannunsa na dama alamar shi ma ya shiga sahun dabbobin dan yana ganin babu yadda za a yi fatallun ta gano shi. Sai da ya ga ya samu waje sannan ya shiga tunano matarsa kuma amaryarsa Talatuwa wacce take can cikin halin naƙuda domin wannan dalilin ne ya sanya ya taho. Hannunsa na hagun ya kai kan kansa tare da fuskarsa zuwa wuyansa ai kuwa ya yi nasarar shafo garin tuwo wanda Talatuwar ta ɗaga ƙwaryar ta juye masa garin a kansa tare da kifa masa ƙwaryar a kansa, duk a cikin halin naƙuda "Kai Talatuwa haka kika mayar da ni kamar an fito da ni daga injin fulawa fari fat babu kyan... Ganin wannan fatallun ta jikin bango tana zamowa ta sakko ƙasa shi ne abin da ya hana Malam Mammani ƙarasa maganar zucin da yake yi. Mai Gari kuwa dama tun lokacin da ya waiwaya ya hangi Malam Mammani ya shigo a tunaninsa fatallunce dan yadda ya gan shi busu-busu da farin abu tun daga kai har fuskarsa wannan ne abin da ya ƙara tsorata shi, sai dai juyawar da ya yi kafin ya juyo sai ya nemi inda fatallun ta yi ya rasa hakan ne ya sanya ya yanke shawarar sakkowa daga saman windown domin ya sama wa kansa maɓoya dan ya ga Gwaggo Ramma bata da niyyar buɗe masa. Yana sakkowa ya tsaya cikin rawar jiki ya ɗaura tazugen wandonsa sabo da ruɗewa sai da ya yi ɗauri bakwai maimakon ya yi ɗaya da azargagiya ɗaya. Wani marayan kukan tausayin kansa ne ya kama shi ganin babu inda zai ɓuya dan ya san ko wajen Salele ya je ba zai saurare shi ya buɗe masa ƙofar ba dan ya ga ko lokacin da suka fara gudun ceton rai har gware suka yi da shi amma ko ya tausaya masa sai ma ya hau gudu ya shige ɗaki ya banko wannan ne ya sanya Mai Gari ya gane cewa yau nafsi-nafsi ake kamar a filin ƙiyama. Durƙusawa ya yi dan ba ya so ya fara tafiya a kan ƙafafunsa fatallu ta ji ƙaran tafiyarsa ta bayyana dn haka rarrafe ya fara duk da yana jin yadda gwiwoyinsa suke gurziwa da ƙurunƙusan tsakuwa amma haka ya daure ya nufi turken dabobi dan ya ga kamar a can ne kaɗai zai samu mafaka tun da yana ganin babu wata fatallu da za ta yi tunanin akwai ɗan adam a wajen dabbobi bare har ta kai masa farmaki. "Kai jama'a! Zawo mai saka manya sauri, wai ni Mai Gari ni ne da rarrafe zan je turken awaki neman mafakar fakewa" Ya faɗa a ransa yana jin tausayin kansa da kansa ganin ba shi da ƴancin shiga ɗaki a ciki gidan. Malam Mammani da yake durƙushe a wajen dabobin yana saƙale da igiyar jigon da ya yi wa kansa a rumfar dabobin tamkar dama nan ne mazauninsa, ganin Mai Gari ya nufo inda yake dan a tunaninsa fatallun ce dan haka sai ya ƙara shan ruwan jikinsa a take jikin nasa ya shiga karkarwa kamar mazari dan bashi da wata nutsuwa da zai gane cewa Mai Gari ne ya nufo wajensa ba fatallun ba. Fitsarin da ya matse shi ne ya kufce masa a take ya fara jin ya ƙara shiga mugun tashin hankali. "Wayyo! Yanzu nan ɗin ma an gudu ba a tsira bane kenan" Ya jefa wa kansa tambayar da ko kusa ba shi da amsar ta. Maman Afrah Whatsapp 09013181851 *META FORCE ARZIƘI DAGA ALLAH* ƳAR UWA SHIN BAKI DA LABARIN META FORCE? DA IRIN ƊINBIM ARZIƘIN DA AKE KWASHEWA A CIKINSA, YA AKA YI BAKI YI REGISTER BA? KO BAKI DA BUƘATAR KUƊAƊEN DA ZA KI YI HIDIMAR YAU DA KULLUM? TO KI ZO NI MAMAN AFRAH NA ZO MIKI DA HANYAR SAMUN KUƊI TA WAYAR HANNUNKI KUƊIN YIN REGISTER KAWAI ZA KI TANADA 9K DUBU TARA DOMIN ANA YIN REGISTER DA DALA 5 NE SAI DAI ALLAH KAƊAI YA SAN IRIN RIBAR DA ZA KI SAMU DA KUMA ALKAIRAN DA YAKE CIKIN KASUWANCIN. IDAN KINA SO SHIGA KUMA DA GASKE KIKE KI MINI MAGANA A WANNAN NUMBER 09013181851 IDAN BA YI ZA KI YI BA KAR KI MINI MAGANA DAN BANA SON ƁATA LOKACI! [8/19, 17:57] Mom mashkur & Afrah: UNGOZOMA (Mai karɓar haihuwa) NA MAMAN AFRAH F. C.W GARGAƊI⚠️ Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ta kowace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowace kafa ba sai da izinina a kiyaye. Page5️⃣➡️6️⃣ Ganin hakan sai Malam Mammani wata dabara ta zo masa a take ya hangame baki ya shiga ƙuga kukan tinkiya sai kukan nasa ya kwatse da na sauran dabbobin wai shi duk a tunaninsa fatallun da ta tunkaro shi ta gane duka dabbobi ne a rumfar babu mutun ko ɗaya. Tun ƙarfi Malam Mammani cewa yake imbeeeee amma Mai Gari ma da yake a ruɗe ba zai ma iya tantance cewar kukan nan ba fa na dabobi bane kaɗai har da na bil adama, dan shi ma ta kansa yake. Malam Mammani da yake ta kukan tunkiya ko saurarawa ba ya yi bai ankara ba sai ji ya yi wani ƙaton rago ya ɗane bayansa, wannan ne ya dakatar da shi daga kukan da ya daddage ƙarfinsa yana yi.Kafin ya gama tantanewa sai jin ragon ya yi ya fara masa barbara. Bai gama dawowa daga mamakin da ya tafi ba sai ya ƙara ganin wani ɗan akuya shi ma ya zo yana sansanar bakinsa. Wani jaririn ɗan tinkiya shi kuma sai ya shiga tura baki jikin rigar Malam Mammani, da alama nono yake nema ya mamula, dibara Malam ɗin ya yi ya tura shi gefe a ransa yana cewa. "Abu ya haɗe mini goma da ashirin in banda lalacewa irin ta dabba har ki kasa banbance uwaki tinkiya da ta kawo ki duniya, ki nufo bil adama kina neman kindirmo(Nono) Ko dan kin jiyo ni ina kukan tumakkai, to ba tunkiya bace Malam Mammani ne, jafa'in fatallu ne ya kawo ni turken dabobi" Ya gama faɗar hakan yana aikawa ɗan tunkiyar harara ganin ɗan tunkiyar ya yi wajjen wata tunkiya yana kuka. "Wuya in ji tsula, ɗan kare ashe ka san uwaka shegantaka ,a ka min" Ya ƙara faɗa a ransa. "Kai jama'a ni rago zai yi wa barbara a tunaninsa ya ɗauka tinkiya ce, ga kuma ɗan akuya a gefe yana neman yi mini kilisa(Kiss) Ya faɗa a ransa a fili kuma sai ya shiga tura mazaunan na shi baya dan ya zame ragon ya faɗi kar ya je ya masa aika-aika. Jin da alama dai rago da gaske kan ƙudurinsa. "Wallahi gwara na yi zamiya ka faɗi a kan ina ji ina gani ka mini fyaɗe, in je in yi ciki cikin ma na shege, shegen ma na dabba wato ɗan rago ko tinkiya" Cewar Malam Mammani a ransa har lokacin yana nan a duƙen sa, gwiwoyin ƙafarsa durƙushe sai kuma tafukan hannayensa da suke a kife ɗaya hannun a saƙale da igiya. Duk tutsun nan da Malam Mammani yake yana ɗaga mazaunai sama sai kuma ya yi ƙasa da su jin ragon ya ƙi janye ƙudurinsa na masa barbara amma ragon ko gezau bai yi ba. Wasu hawaye masu ɗimi rigis ne suka gangarowa Malam ɗin tare da wani kuka marar sauti. Mai Gari bai lura da Malam Mammani ba, dan haka shi ma yana ta ƙoƙarin ɓoye kansa ne a cikin dabobin, Malam Mammani kuwa gabaɗaya tashin hankalinsa ya linku jin rago yana masa barbara ga kuma kallon fatallun da yake yi wa Mai Gari dan haka sai ya danne kukan nasa ya buɗe baki domin ya cigaba da kwaɗa kukan tinkiya dan kar fatallun ta gane cewa shi bil adama ne ta cutar da shi dan haka sai ya hangame baki da shaƙyaƙƙiyar murya ya cigaba da kukan tinkiya suka haɗu da kukan sauran dabbobin ba tare da Mai Gari ya fuskanci wani abu ba. Malam Ganin Mai Gari yana dogon wuyan da ya kasa gane leƙen mai yake, dan dai a ransa yana ta tunanin dama su ma fatallum suna jin tsoro ne? Ganin kamar fatallun ma a tsorace take. A hankali Mai Gari ya zame ya kwanta a ƙasa cikin takin dabobin da rubda ciki ya kwanta tamkar yadda sojoji suke yi idan za su yi harbi in suna bakin daga. Bayan ya kwanta sai shi ma ya buɗe baki ya shiga kukan akuya, mamaki ne ya cika Malam Mammani ya ma rasa ma'aunin hankalin da zai ajiye al'amarin. "To fa! Abin na Allah ne budurwa da ciki gwaro da yaye, ai da ganin wannan abin ba zai iyu ba auren ɓera da mage in banda abin banza hanci babu ƙafa ya za a yi ni ina jin tsoron fatalwa ita ma fatalwar tana jin tsoro, in banda ma sabon salo kiran sallah da usur ya za a yi fatallu take kukan dabobi... Ƙafar Mai Gari ce da ta zunguri Malam Mammani hakan ne ya sanya tunanin Malam ɗin tsayawa cak! Wani tsoro ya baibaye shi jin kofaton ƙafar fatallu ta taɓa shi, a take wani guntun fitsari da ya maƙale ya shiga zubowa kamar an buɗe lalataccen famfo. "Oh ni Mammani, abin daga Allah yake matar takaba ta yi ciki, yo abin duniya mene ne ? Kaza ta jawo muzuru kwanan gida" Cewar Malam Mammani a zuciyarsa yana fatan ƙasa ta tsage ya shige ciki ko ya samu salama daga wannan uku bala'in da yake ciki. Mai Gari kuwa jin ya zunguri wani abu kamar jikin mutum dan ya ji abin da ya taɓa babu gashi ko kaɗan bare ya yi zaton jikin dabba ne, ai a take ya dakata daga kukan akuyar da ya fara ya maƙure a waje ɗaya wani tsoron yana turnuƙe shi jin ashe dai an gudu ne ba a tsira ba tun da ga shi ya ɓuya a turƙen dabobi amma kuma ashe dai ya kashe miciji ne bai fitar masa kansa ba tun da ga shi dai fatallun ta riga shi isa turken dabobi. "Almuhaiminu, Aljabbaru, Almutakabbiru" Mai Gari ya shiga jero subayen Allah, domin ya ji faɗuqae gabansa da tsoron da yake ciki suna hauhawa kamar fulawar da aka kwaɓa da yis. Gwaggo Ramma da take cikin duro ɗin dawa jin kukan dabobi ya kwamutsa da na mutane sai kawai ta cigaba da kukan tausayin kanta, domin hakan ya tabbatar mata akwai wata gagarumar matsala, tun da ta san dai mutum ɗaya ne a waje wato mijinta dan tun kukan da ya saki ta fahimci Salele bai bar Mai Garin ya shiga ɗakinsa ba,amma kuma yanzu tana iya jiyo kukan ba na mutum ɗaya bane domin abin da ya fi ɗaure mata kai ma ne yadda take iya tsinkayo kukan mutanen kamar dai kukan dabobi suke yi. Ƙara takure kanta ta yi a cikin duron tana ƙara gyara zaman fantekar da ta kifa a kanta, kafin daga bisani ta shiga ambaton. "Ƙuliya ayyuhal kafirun, li'ilafi ƙuraishin, inna anzalnahu fi lailaitil ƙadr" Haka take jero karatun tana rawar ɗari tamkar mai cutar masassara duk da ba wai tana jeranta ayoyin bane sai dai kawai ta tsinto waccan ayar a cikin wata sura sai ta ƙara ɗakko ra wata surar amma ita a ganinta daidai take yi wai tsoho ya durƙusa ya gaishe da yaro. Salele ma shi tsabar shiga tashin hankali bai san lokacin da ya tashi zaune ba daga kwancen da yake sai gani ya yi ya fara dungura goshinsa a kan katalalliyar katifarsa alamar sujada dan ya ga dai karatun ya gagare shi. "Gwara in ke yin sallar ko iya sujadar kaɗai na yi Allah ya ga niyyata, sallolin yau karkaf nake haɗa wa yanzu gudun kar in mutu mala'iku su tisa ƙeyata zuwa wuta" Ya faɗa a ransa dan shi a yau ko sallah ɗaya bai yi ba daga cikin farillan salloli guda biyar dan shi ba ya ƙaunar yin sallah sai yanzu da ya ga mutuwa tana neman zuwa ɗaukansa shi ne ya fara gabatar da sallolin ta hanyar yin sujada. "Anya Salele sallar nan taka za ta karɓu kuwa? Kai da ko alwala baka yi ba hasali ma ɗazu ka shiga bayi ka gandara kashinka" Wani sashe na zuciyarsa ya faɗa. "Allah ka yafe mini ni bansan ma iya adadin raka,'o in da zan yi ba a salloli bakwai ɗin nan ban san kowacce raka'a nawa ake yi ba, sai dai in yi ta yin sujjadar iyaka iyawa ta" Ya ƙara faɗa a ransa dan shi sabo da rashin zuwa makarantar arabi ma bai san adadin sallolin da ake yi a rana ba bare har ya san raka'o'in su. Haka ya shiga dungura sujjadar da yake wacce daga ya ɗora goshin sa sai ya ɗago da sauri kamar ya ɗora a kan wuta, ba komai ya kawo hakan ba sai rashin nutsuwa da tashin hankali da yake ciki. Malam Mammani jin an taɓa shi sai gabansa ya shiga dakan lugude, a take ya ji wani tsoron ya linku a kan wanda yake ji ga kuma barbarar da ragon nan yake masa a ransa dan yana ganin shi ba tinkiya ba ya za a yi rago yake masa barbara dan yana jin har da fitsari ragon ya masa. Hannunsa na hagu ya miƙa ya farɗo ƙafar ragon cikin ƙarfin hali ya janyo shi, sai ga rago ya dawo gaban Malam Mammani da yake durƙushe baki yana mismis alamar addu'a. Mai Gari kuwa ƙafar ragon ce ta sauka a kan ɗan yatsunsa da suke wurin wani zafi da raɗaɗin yadda kofaton ragon ya ratsa hannunsa, a take wani inu ya ƙwace masa da bai san lokacin da ya saki ihun ba tare da wani guntun fitsarin wahala. Ihun Mai Gari shi ya ƙara razana Malam Mammani a take Malam Mammani ya kaiwa wata akuya cafka da hannu ɗaya ba ya rungumeta bai san lokacin da ya fara faɗin "Iya ki taimaka mini ga fatallu nan" Ya faɗa cikin gushewar hankali. Mai Gari jin furucin nan sai ya ƙara ruɗewa bai san lokacin da ya firgita ba sai ga shi ya ƙwaƙumo Malam Mammani cikin rashin sanin inda ya damƙa a take tsoro ya game musu zuciya su duka dan kowa ya ji ya rungumi mutum a tare kuma a lokaci guda suka saki wata tusa mai ƙara kamar bugun shantu. Mai Gari fuskar da ya ɗago sai ya sauke a kan fuskar Malam Mammani da ta sha garin tuwo ta ƙoshi sai kuwa ya ganshi tamkar fatallun ga kan nan nashi da ya sha askin tanƙwal ya yi buɗuɗu da farin garin tamkar an shafawa biri fulawa. Jikin Mai Gari ne ya shiga karkarwa tamkar an jona shi da wutar lantarki dan shi dai ya ji ya taɓa abu ɗazu amma ganin fuskar nan ta saka shi a tashin hankalin da bai shiga rabinsa ba ɗazu. Abin da yake saka shi ƙara shiga kogin mamaki bai wuce yadda jikin Malam Mammanin da yake tunanin fatallu bace yake karkarwar da ya fara tunanin ta fi wacce jikinsa yake. Gwagwarammmmmm Wani sautin yadda aka buga ƙofar gidan har ta bugu da bango ta koma aka sake banko ta shi ne abin da ya saka Malam Mammani sakin akuyar da ya daƙuma ya fara kiciniyar ƙwace kansa daga riƙon da Mai Gari ya masa. "Fatallu ki mini rai dan Allah wallahi matata ce take naƙuda shi ne na fito kirawo mata UNGOZOMA" Malam Mammani ya furta cikin jin tsoro dan bai san ba ma maganganun suna rige-rige fitowa ba sai da ya ji ya fesar da su sannan ya fahimci abin da ya yi. Bugun zuciya da kuma numfashin Mai Gari ne suka tsaya cak, jin muryar Malam Mammani maƙocin gidansa da ya taso mamaki al'ajabi ne suka baibaye masa zuciya tambayoyi fal bakinsa yana son ya amayar da sh. "Malam Mammani!!! " Ya ambaci hakan a zuciyarsa. Ƙaran wani abu kamar dirifkiya shi ne ya dakatar da Mai Gari da kuma Malam Mammani suka shiga jin bugun zuciya a hankali suka ji ƙaran yana ƙara shigowa cikin wanda suka ji tamkar da ƙafafu a ke. Wani hasken fitila ne ya gauraye gidan wanda ya haske har wajen dabbobin da su Malam suke. Kallon kallo aka shiga yi tsakanin Malam Mammani da Mai Gari, da sauri Mai Gari ya saka hannu ya shafo fuskar Malam Mammani ya ce "Malam Mammani" Ya faɗa a ransa. Shi ma Malam Mammani baki sai lokacin hasken fitilar da aka haska ya ganar da shi cewa Mai Gari ne, sai dai su duka basu gama dawo wa daga mamaki ba sai kawai tsoro ya yi wa zukatansu ƙawanya, ganin mai haska fitilar ya haska musu wata ƙatuwar mata wacce ƙibarta ta wuce misali kuma ƴar duƙurƙusa bata da tsayi ko kaɗan dan tsawonta bai fi tsawon buhun gero ba. A tare cikinsu ya murɗa kafin su dawo daga tsoron da firgicin sai kawai mai haska fitilar ya mayar da akalar hasken zuwa ƙafafunsa, su duka idanu suka zaro ganin ƙafarsa sanye yake cikin kayan sojoji a haka ya cigaba da haska wa har zuwa fuskarsa. n "Taju" Suka haɗa baki wajen faɗa a fili. Asalin labari Mai Gari Kailu, shi ne asalin sunan Mai Gari yana da mata ɗaya mai suna Ramma ana kiranta da Gwaggo Ramma. Ƴar su ɗaya Habiba wacce ta rasu wajen haihuwar jikansu Salele, ƴaƴan Habiba biyu Tajuddin shi ne babba sai kuma Salele. Gwaggo Ramma ƴa ce ga wani hamshaƙin bokan yankin na ƙauyan Gumurzu, mai suna Boka Mai Zilli, wanda babu abin da ya iya sai tsubbu da bokanci, cikin sana'ar bokancin nasa ne ya ba wa ƴarsa Ramma laƙanin INGOZOMANCI domin take karɓar haihuwa a kaf ƙauyan hakan a matsayin jarin da za ta yi sana'a. Hakan kuwa aka yi har ya koma ga Allah Gwaggo Ramma ce take karɓar haihuwar kowace mace da take cikin garin Gumurzu da sauran ƙauyukan yankin dan ko mace za ta mutu idan tana naƙuda, to babu wanda zai taimaka mata ta haihu sai dai a nemo Gwaggo Ramma. Taju da Salele sun kasance yara ne marar sa ji, sai dai shi Salele ba ya ƙaunar karatu da zuwa makaranta, inda suka sha banban da Taju da yake son zuwa makaranta musamman ta boko sabo da yana so ya zama soja. Bayan ya kammala sakandire ya ce ya tafi birni domin ya je ya samo aikin soja tun da ya tafi sama da shekara guda sai yau ya dawo. MAMAN AFRAH WHATSAPP 09013181851 *META FORCE ARZIƘI DAGA ALLAH* ƳAR UWA SHIN BAKI DA LABARIN META FORCE? DA IRIN ƊINBIM ARZIƘIN DA AKE KWASHEWA A CIKINSA, YA AKA YI BAKI YI REGISTER BA? KO BAKI DA BUƘATAR KUƊAƊEN DA ZA KI YI HIDIMAR YAU DA KULLUM? TO KI ZO NI MAMAN AFRAH NA ZO MIKI DA HANYAR SAMUN KUƊI TA WAYAR HANNUNKI KUƊIN YIN REGISTER KAWAI ZA KI TANADA 9K DUBU TARA DOMIN ANA YIN REGISTER DA DALA 5 NE SAI DAI ALLAH KAƊAI YA SAN IRIN RIBAR DA ZA KI SAMU DA KUMA ALKAIRAN DA YAKE CIKIN KASUWANCIN. IDAN KINA SO SHIGA KUMA DA GASKE KIKE KI MINI MAGANA A WANNAN NUMBER 09013181851 IDAN BA YI ZA KI YI BA KAR KI MINI MAGANA DAN BANA SON ƁATA LOKACI! [8/19, 17:57] Mom mashkur & Afrah: INGOZOMA (Mai karɓar haihuwa) NA MAMAN AFRAH F.C.W GARGAƊI⚠️ Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ta kowace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowace kafa ba sai da izinina a kiyaye. Page 7️⃣➡️8️⃣ *Dawo wa daga labari.* Tsoron da su Malam Mammani suke ji ne ya ragu ganin Taju da kayan sojoji sun san kuwa dole fatallu ta ji tsoron bindiga. Wata ajiyar zuciya mai ƙarfi suka saki a tare dan suna ganin ai kakarsu ta yanke saƙa. "Mamaki kwalli a kunne, yau kuma Taju ne ya dawo" Mai Gari ya faɗa a ransa cikin murna dan babu wani abu da ya daɗaɗa masa rai sama da ganin Taju da kayan sojoji kuma a lokacin da yake cikin halin buƙatar taimako. Cikin sauri Malam Mammani da Mai Gari suka shiga ƙoƙarin tashi sai dai Malam Mammani gabaɗaya ya sha'afa da hannunsa na dama da ke ƙulle a jigon dabobi dan haka zai tashi tsaye sai ya ji hannun a maƙale a take ya shiga fitar da hannun dan yanzu tun da halin da suke ciki ya zo ƙarshe to kuwa burinsa bai wuce ya gan shi a gaban matarsa da ya baro ta a cikin halin naƙuda ba. Mai Gari ko ta kan Malam Mammani bai bi ba ya nufi wajen su Taju har yana neman yin tuntuɓe, dan shi yana ganin shikenan waraka ta zo masa wai mazaunan matar mai bayar da maganin wuta ya ƙone. "Taju, taɓ lallai abu rabo ne tsintar ƙwan jaki, kai ne wannan" Ya faɗa yana dab da ƙarasowa wajen su Taju har ya kusa ƙarasa wa kamar wanda aka ce ya tsaya ai kuwa ya ja tunga ya shiga rafkawa Gwaggo Ramma kira. "Ramma! Ramma! Ramma, Salele, Salele Salelee" Mai Gari da ya wawake dogon maƙogwaronsa ya shiga faɗa ko jan numfashi ba ya yi. "Kai jama'a, a yi a gama ai ya fi a ƙarasa gobe, in banda dai lokacin da mage take wuri ɓera ba ya wasa ta yaya kai da kake hannun fatallu za ka shiga kiran sunana son a gano maɓoyata a zo a tafi da ni to wallahi ta Allah ba taka ba, dan wallahi sai dai a yi abin da za a yi wai mahaukaci ya ɗau rigar kura dan wallahi wanda za shi sama ya taka leda haƙiƙa ya ci ƙarfin tafiya kuma nan gani nan bari farar tumfafiya" Cewar Gwaggo Ramma tana ciko hannunta taf da dawar cikin duron da take ciki ta tura a bakinta, ta ƙara cunkusowa ta ƙara cusawa a bakin wai duk dan gudun kar ma ta yi suɓutar baki ta yi magana a jiyo ta. Ko kuma Mai Gari ya yi abin da za ta tausaya masa kar ta yi magana. "Ramma" Ta ƙara tsinkayar muryarsa tamkar dai ba a tsakiyar dare yake kiran ba. "Ka yi haƙuri Mai Gari tun da dai sa'i ya yi to sai dai mu ce Allah rahama maka, ya kai haske kabarinka, kuma mundahanar da ka sha yi da kayan jama'a talakawanka sai dai in ce Allah yafe maka" Ta faɗa a ranta lokacin da ta ji dawar bakinta wata har tana wuce mata maƙogwaro amma dan ƙarfin hali haka ta cigaba da daurewa dan a kan ta fito fatallu ta yi watanda da namanta ko ta kashe ta ma lokaci guda gwara ta cigaba da zama a cikin dawar. Dan da ta ji ma kiran Mai Garin yana ƙara kaɗa mata hanjin cikinta sai ta cusa fuskarta a cikin dawar ya zamana numfashi ma dakyar take shaƙa. Mai Gari kuwa jin Gwaggo bata amsa ba sai ya ƙara mayar da akalar kiran kwacakwam ga Salele. Salele da yake ta faman yin sujada a kan katifarsa har lokacin bai dakata ba, dan yanzu ko shi kansa bai san iya adadin sujadar da ya yi ba, jin muryar kankansa Mai Gari yana kiran sunnansa a take ya kasa dungura goshin nasa. "Wallahi kai dai mutumin nan an yi ɗan nema wallahi, haka kawai dan son ka ɓallo mini ruwa za kake kirana kuna can cikin halin ƙaƙanika yi, ai tun da dai ku kaɗai fatallun ta gani sai ku haƙura ku tafi lahirar ku kaɗai" Ya faɗa yana fara lallaɓawa ya je can inda yake ajiye takalman ball ɗinsa yana zuwa ya miƙa hannu ya ja mazugin takalmin ya zugi tamkar zai saka takalmin a ƙafarsa amma abin mamaki sai ya durƙusa ya saka fuskarsa a kan takalmin yana ƙoƙarin saka kansa a cikin takalmi. "Dan Allah kaina ka mini rai ka shige cikin takalmin nan na ƴan ball, ka cece ni na tsira da mutuncina, in shiga cikin ka in laɓe sai ƙura ta lafa na fito" Ya faɗa har lokacin yana ƙoƙarin ganin kan nasa ya shige cikin takalmi dan sai dannawa yake bayan gabaɗaya ma ko faɗin fuskarsa bai shiga ciki ba. "Allah ka bani layar zana in ɓace in huta, Allah na tuba ka yafe mini kura-kuraina zan cigaba da yin sallah" Ya faɗa yana ɗaga hannu sama alamar addu'a idanunsa suna zubar hawaye. "Allah ka sa in koma kamar ɓera ko ma kiyashi yadda zan ɓuya ba tare da an ga mafaka ta ba" Ya faɗa hawaye suna kwaranyo masa tamkar an buɗe famfo. "Yeeee jama' a ku fito Tajuddin ya dawo sanye da kayan sojoji shikenan mun warke" Cewar Mai Gari da ƙarfi dan ya ga idan ba haka ya yi ba babu wanda zai fito. Ɗif Gwaggo ta yi fuska a cikin dawa. "Ikon Allah na zaune ya faɗi, Taju kuma? Allah sarki Mai Gari kin dai ji yana mini albishir mai daɗi, ya ɗauka ban san na rufe masa ƙofa ba ni kuwa ina sane wai karuwa ta taka matar aure" Ta faɗa a zuciyarta, a take ta yi jifa da fantekar kanta bizigir ta fito daga cikin duron har zaninta yana neman faɗuwa ta kama ta ɗaura. "Kai dai zanin nan nawa kana son a ke ganin tsiraicina, in ba haka ba da yaushe ma na ɗauraka" "Allah sarki ashe dai rai kan ga rai, lallai in da rai da rabo yo ni yanzu ina na ga ta zama wai an ɗaurawa karya zane" Ta faɗa tana fitowa ta buɗe ƙofar ta fito dan sai da ma ta leƙo ta windown ta tabbatar ganin wata dalleliyar fitila. Salele ma bai san ma ya sauke hannuwansa ba, daga ɗaga wa da ya yi yana addu'ar, jin an ce Taju ya dawo. A sukwane ya buɗe ƙofar ya bazamo yana tahowa da sauri har yana tuntuɓehaka ya fito yana haɗa wa da gudu, Kusan a tare suka fito shi da Gwaggo, Malam Mammani ma da ya hango Gwaggo sai ya ji matsalarsa ta zo ƙarshe tun da ga Gwaggo sai su tafi ta karɓi haihuwar amaryarsa Shamsiya. Dan haka shi ma cikin zafin nama ya taho daga turken dabobin da wani jargaggaɓin wandonsa da ya sha fitsari sama da cikin kwando. Fara gudunsa kenan wani ƙaton rago mai manyan ƙaho ya tunguje Malam Mammani sai ga Malam Mammani tamkar iska ta ɗaga leda ya faɗi yashe a wurin ya ji faɗuwar sosai amma sabo da ganin INGOZOMA sai ya yi ta maza ya tashi tsaye ya taho da gudu. Mai Gari ma ganin sun yi ayari kowa ya nufi wajen Taju sai shi ma gudun kar a yi babu shi, amma shi gogan da yake riƙe da fitilar nan ko motsi bai yi ba kamar ma bai san ana yi ba wai kunu a maƙota. "Kai!!!" Matar nan da take tsaye daga gefen Taju ta faɗa da mugun ƙarfi wanda hakan ya sanya su duka suka dakata. Cikin tsananin mamaki Gwaggo ta saki baki dan ita har ga Allah bata lura da matar ba ma, da yake hasken duk ya dalle mata idanu. Su duka huɗun sai yanzu suka yi wa matar kallon nutsuwa, mace ce gabjejiya dan ko za a jaɗe su, su duka huɗun kar in ma za a haɗa har Taju to ba za su kai girman rabin jikinta ba ma. Dan faɗin jikinta tamkar ka haɗa buhun gero biyu ne, girmanta ma ya wuce misali Sai shegen gajarta kamar wata wada. "Taju ka cigaba da aikin ka" Ta faɗa da kakkausar murya, hakan ya sanya su Mai Gari sakin baki kamar layar mai tafiya suna kallonta. Taju kuwa a take ya fara buga ƙafafu yadda sojoji suke yi, ya sara mata kafin daga bisani kuma ya fara fareti yana ta yi yana faɗin "Left right" Tamkar zai ari baki. "Ku in banda ku sakarkaru ne, kuma ma banda sakarci waƙa a tasha haka kuka fito kuna wani gudu tamkar wasu shanaye, shin baku ganni bane? Ko an ce muku bakin rijiya wajan wasan makaho ne? To ku buɗe kunnuwanku ku ji ni, hatta Taju da kuke gani a ƙarƙashin ikona yake dan haka kowa ya iya bakinsa domin bahaushe ya ce iya ruwa fidda kai" Cewar tiƙeƙiyar matar nan cikin wata irin murya mai kama da ta ƴan bariki. "Haba ke kuwa baiwar Allah, yanzu a talatainin daren nan duk da an ce dare mahutar bawa ne amma za ki zo ki nemi ki ɗaga mana hankali, muna cikin tsoron zuwan fatallun ashe dai bonono ne muka yi wai rufin ƙofa da ɓarawo" Gwaggo Ramma ta faɗa tana tafa hannuwa duk da irin dukan luguden da ƙirjinta yake na tsabar tsananin tsoron ƙatuwar matar da tun da uwarta ta haifeta bata taɓa ganin halitta mai girman wannan ba, dan idan akwai wani abu da za a kwatanta da matar to kuwa sai dai a kwatanta ta da giwa, dan tsawo kawai giwa za ta faɗa wa matar. Kuma abin da ya ƙara sanyaya musu jiki irin yadda take ba Taju umarni duk da kayan sojojin da yake jikinsa hakan ne ya sanya suka kasa banbance aya da tsakuwa. "Au Allah har kina da bakin magana to ki sanya a ranki daga yau kun yi ban kwana da zaman lafiya ke hatta dare da rana zai zama ɗaya a wajenku" Matar ta faɗa tana kallonsu. "Haba gingimemiya wai ya haka ne, za ki zo ki yi wani tiƙiƙi da ke kina mana wasu maganganu mararsa kai da ƙaf... Wani mari da ƙatuwar matar nan ta ɗauke Salele da shi, shi ne ya dakatar da shi daga maganar da bai ƙarasa ba. Ƙaran marin ne ya sanya Gwaggo da Mai Gari, juyawa a kiɗime za su koma ɗaki har zanin Gwaggo yana neman faɗuwa ta taro shi. "Duk wanda ya ƙara ɗaga ƙafarsa daga nan sai ya gwammace kiɗa da karatu" Tun kan matar ta ida maganar Gwaggo da Mai Gari suka ja wani uban birki tamkar motar da ta kusa hantsilawa rami ta yi birki. Taju kuwa ganin hukunci da aka yi wa ƙaninsa na mari sai ya bada himma wajen cibaga da faretin da yake yi har ƙara ƙuga "Left right ɗin yake. Salele kuwa marin da aka masa sai da ya ga gilawar taurari masu mugun haske, sannan sai idanun nasa suka yi wani dilim ya daina ganin komai, sai kuma ganinsa ya dawo zafin marin kuwa sai da ya saka shi sakin fitsari a wando. Malam Mammani kuwa a take ya shiga janyo salatin annabi bakinsa banda mismis babu abin da yake dan shi ya tabbatar da shi aka ɗauke da marin to da kuwa idan suma ne ma da ya yi dan yana jin ko zai falka daga suman wataƙila sai ya yi wata bakwai ko sama da haka dan ya ga yanayin jikin matar nan akwai matsala a ce ko lakucin mutum ta yi bare kuma mari. Ɗif gidan ya yi tamkar babu wata halitta a ciki, baka jin komai sai ƙaran faretin Taju da left right da yake faɗa. "Ko akwai mai magana ? Idan akwai ina sauraro dan ni wandon roba nake daidai da ƙugun kowa, duk abin wani zai yi to abin zai zo min a daidai wai mai ido ɗaya ya leƙa kwalba" Ta faɗa tana ƙoƙarin ɗaga ƙafafunta kowa kallonta kawai yake yana mamakin irin ƙibarta, ita kuwa ko a jikinta wai an tsikari kakkausa dan ta san ƙibar nan tata ita ce take ceton ta. Malam Mammani hawaye ya fara na tausayin matarsa ya san ana can ana jiran zuwansa da INGOZOMA amma kuma ga shi daga shi har INGOZOMAR a cikin wani hali. "Taju dakata da aikin nan" Kafin ta rufe bakinta ƙafafun Taju sun tsaya daga faretin, nakinsa ma ya yi ɗif kamar an yi ruwa an ƙafe lunfashinsa ne kaɗai yake aiki a jikinsa dan ya ƙame a waje ɗaya sai hannunsa da ke gefen kunnensa wanda ya sara mata irin yadda sojoji suke sarawa na sama da su. Taju ina so ka faɗa musu wacece ni" "Su ,su, su" "Ka nutsu dalla! Bana son wata in'inna" Ta faɗa tamkar za ta kai masa duka, da sauri ya saita nutsuwarsa ya fara bayani. "Sunan ta yallaɓiya Laila, matar shugaban ƙasar sojojin duniya, tana da ɗa mai suna Nasiru" Ya faɗa yana ƙara daidata nutsuwarsa dan ba ya so ko kaɗan ya yi katoɓara daga bayanin da ta masa abin da zai samu hukunci daga wajenta dan da a ce ta hukunta shi gwara a bashi aikin ƙarfi na sati guda. "Zan zauna da ku na tsawon lukuta ni kaina ban san lokacin tafiyata ba... Dididim diiimmm Gaban Mai Gari Salele, da kuma Gwaggo ya buga jin wai zama za ta yi a gidan bata san ranar tafiyarta ba lallai akwai gwarama. "Taɓɗi! Sha biyun dare marecan kura, ai ni da zuwa gidan nan sai ranar da kika bar gidan nan" Cewar Malam Mammani a ransa yana fatan Allah ya kuɓutar da shi daga gidan. "Ba na son a ke barina da yunwa ko ni ko ɗana, sannan a kowace rana ina cin shinkafa kwano biyar da rana, kai a taƙaice ma a rana ban san iyakacin abin da nake ci ba dan haka a kiyaye, sannan idan lokaci tusa ta ya yi ba na iya yin tusa sai na zauna a kan mutum, sannan tusar take samun damar fitowa, dan haka a duk lokacin da zan yi tusa zan ƙwalawa ɗaya daga cikin ku kira sai ya zo na zauna a kansa na saki tusa ta" Ƙulululuuuuuu, cikin Mai Gari da Gwaggo ya bada, cikin Salele kuwa ya fi na kowa murɗawa saboda ya san yanzun nan matar iya hannu kaɗai ta sa ta mare shi sai da ya gwammace kiɗa da karatu bare kuma a ce ta danne mutum ai sai mutuwa kuma. Malam Mammani kuwa dariyar ƙeta ya fara a zuciyarsa jin wai sai an danne su Mai Gari za a ke yin tusa tabbas ya san za a sha dirama ba ƴar kaɗan ba a gidan. "Allah ya kawo wa jama'ar garin Gumurzu wacce za ta rama musu cuta da cin zalin da Ramma da Mai Gari suke yi" Ya faɗa a ransa yana godewa Allah dan ya san tabbas matar nan sai ta gyara musu zama musamman Mai Gari da ba shi da aiki sai karɓe gonaki da abincin mutane da suka noma kai babu wani abu da Mai Gari ba ya karɓa a hannun mutanensa. MMn Afrah Wtsapp 09013181851 *META FORCE ARZIƘI DAGA ALLAH* ƳAR UWA SHIN BAKI DA LABARIN META FORCE? DA IRIN ƊINBIM ARZIƘIN DA AKE KWASHEWA A CIKINSA, YA AKA YI BAKI YI REGISTER BA? KO BAKI DA BUƘATAR KUƊAƊEN DA ZA KI YI HIDIMAR YAU DA KULLUM? TO KI ZO NI MAMAN AFRAH NA ZO MIKI DA HANYAR SAMUN KUƊI TA WAYAR HANNUNKI KUƊIN YIN REGISTER KAWAI ZA KI TANADA 9K DUBU TARA DOMIN ANA YIN REGISTER DA DALA 5 NE SAI DAI ALLAH KAƊAI YA SAN IRIN RIBAR DA ZA KI SAMU DA KUMA ALKAIRAN DA YAKE CIKIN KASUWANCIN. IDAN KINA SO SHIGA KUMA DA GASKE KIKE KI MINI MAGANA A WANNAN NUMBER 09013181851 IDAN BA YI ZA KI YI BA KAR KI MINI MAGANA DAN BANA SON ƁATA LOKACI! MASU MINI MAGANA KAN HARKAR META FORCE SUNA YIN REGISTER, INA MUKU FATAN ALKAIRI INA TAYA KU MURNA DA SHIGOWA GIDAN ARZIƘI ALLAH SA AN FARA A SA'A🥰 [8/19, 17:57] Mom mashkur & Afrah: UNGOZOMA (Mai karɓar haihuwa) NA MAMAN AFRAH F.C.W GARGAƊI⚠️ Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ta kowace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowace kafa ba sai da izinina a kiyaye. Wannan tallar hajar mata masu aji ce💃 Ina mata ƴan ƙwalisa, babbar mace alkyabbar mata, macen mai gyara ita wacce ta isa da miji su o'o sai dai su ga ƙeyar mijinta idan ya wuce amma basu ishe shi kallo ba domin babu abin da za su nuna mata. Gyaran gashi babbar martaba ce da take ɗaga darajar mace, musamman kayan gyaran gashin MAMAN ZEE da ya yi fice a ko ina ake labarinsa. Gani ya kori ji sai an gwada akan san na ƙwarai siyan na gari mayar da kuɗi gida💃💃💃💃💃💃💃💃 Hadaddu Kuma ingantattun kayan gyaran gashin mamanzee(chebe hair set) Wadanda suke dawowa da martabar gashin Kai komai lalacewarsa biiznillahi Rabbi Ga kyau ga inganci ga saukin kudi muddin kika fara amfani da kayammu sekindawo Mana da kyakkyawan labari Kanki zeyi kyau ya rika sheki yayi tsayi yayi laushi duk matsalar da ke cikin kanki zata kau in sha Allah Munada set complete Kuma Muna Bada pieces Haka Kuma Muna Bada Sari Muna turawa akowanne gari kike Kuma Ako wacce kasa kike Phone number *08079130166* Page 7️⃣➡️8️⃣ *Dawo wa daga labari.* Tsoron da su Malam Mammani suke ji ne ya ragu ganin Taju da kayan sojoji sun san kuwa dole fatallu ta ji tsoron bindiga. Wata ajiyar zuciya mai ƙarfi suka saki a tare dan suna ganin ai kakarsu ta yanke saƙa. "Mamaki kwalli a kunne, yau kuma Taju ne ya dawo" Mai Gari ya faɗa a ransa cikin murna dan babu wani abu da ya daɗaɗa masa rai sama da ganin Taju da kayan sojoji kuma a lokacin da yake cikin halin buƙatar taimako. Cikin sauri Malam Mammani da Mai Gari suka shiga ƙoƙarin tashi sai dai Malam Mammani gabaɗaya ya sha'afa da hannunsa na dama da ke ƙulle a jigon dabobi dan haka zai tashi tsaye sai ya ji hannun a maƙale a take ya shiga fitar da hannun dan yanzu tun da halin da suke ciki ya zo ƙarshe to kuwa burinsa bai wuce ya gan shi a gaban matarsa da ya baro ta a cikin halin naƙuda ba. Mai Gari ko ta kan Malam Mammani bai bi ba ya nufi wajen su Taju har yana neman yin tuntuɓe, dan shi yana ganin shikenan waraka ta zo masa wai mazaunan matar mai bayar da maganin wuta ya ƙone. "Taju, taɓ lallai abu rabo ne tsintar ƙwan jaki, kai ne wannan" Ya faɗa yana dab da ƙarasowa wajen su Taju har ya kusa ƙarasa wa kamar wanda aka ce ya tsaya ai kuwa ya ja tunga ya shiga rafkawa Gwaggo Ramma kira. "Ramma! Ramma! Ramma, Salele, Salele Salelee" Mai Gari da ya wawake dogon maƙogwaronsa ya shiga faɗa ko jan numfashi ba ya yi. "Kai jama'a, a yi a gama ai ya fi a ƙarasa gobe, in banda dai lokacin da mage take wuri ɓera ba ya wasa ta yaya kai da kake hannun fatallu za ka shiga kiran sunana son a gano maɓoyata a zo a tafi da ni to wallahi ta Allah ba taka ba, dan wallahi sai dai a yi abin da za a yi wai mahaukaci ya ɗau rigar kura dan wallahi wanda za shi sama ya taka leda haƙiƙa ya ci ƙarfin tafiya kuma nan gani nan bari farar tumfafiya" Cewar Gwaggo Ramma tana ciko hannunta taf da dawar cikin duron da take ciki ta tura a bakinta, ta ƙara cunkusowa ta ƙara cusawa a bakin wai duk dan gudun kar ma ta yi suɓutar baki ta yi magana a jiyo ta. Ko kuma Mai Gari ya yi abin da za ta tausaya masa kar ta yi magana. "Ramma" Ta ƙara tsinkayar muryarsa tamkar dai ba a tsakiyar dare yake kiran ba. "Ka yi haƙuri Mai Gari tun da dai sa'i ya yi to sai dai mu ce Allah rahama maka, ya kai haske kabarinka, kuma mundahanar da ka sha yi da kayan jama'a talakawanka sai dai in ce Allah yafe maka" Ta faɗa a ranta lokacin da ta ji dawar bakinta wata har tana wuce mata maƙogwaro amma dan ƙarfin hali haka ta cigaba da daurewa dan a kan ta fito fatallu ta yi watanda da namanta ko ta kashe ta ma lokaci guda gwara ta cigaba da zama a cikin dawar. Dan da ta ji ma kiran Mai Garin yana ƙara kaɗa mata hanjin cikinta sai ta cusa fuskarta a cikin dawar ya zamana numfashi ma dakyar take shaƙa. Mai Gari kuwa jin Gwaggo bata amsa ba sai ya ƙara mayar da akalar kiran kwacakwam ga Salele. Salele da yake ta faman yin sujada a kan katifarsa har lokacin bai dakata ba, dan yanzu ko shi kansa bai san iya adadin sujadar da ya yi ba, jin muryar kankansa Mai Gari yana kiran sunnansa a take ya kasa dungura goshin nasa. "Wallahi kai dai mutumin nan an yi ɗan nema wallahi, haka kawai dan son ka ɓallo mini ruwa za kake kirana kuna can cikin halin ƙaƙanika yi, ai tun da dai ku kaɗai fatallun ta gani sai ku haƙura ku tafi lahirar ku kaɗai" Ya faɗa yana fara lallaɓawa ya je can inda yake ajiye takalman ball ɗinsa yana zuwa ya miƙa hannu ya ja mazugin takalmin ya zugi tamkar zai saka takalmin a ƙafarsa amma abin mamaki sai ya durƙusa ya saka fuskarsa a kan takalmin yana ƙoƙarin saka kansa a cikin takalmi. "Dan Allah kaina ka mini rai ka shige cikin takalmin nan na ƴan ball, ka cece ni na tsira da mutuncina, in shiga cikin ka in laɓe sai ƙura ta lafa na fito" Ya faɗa har lokacin yana ƙoƙarin ganin kan nasa ya shige cikin takalmi dan sai dannawa yake bayan gabaɗaya ma ko faɗin fuskarsa bai shiga ciki ba. "Allah ka bani layar zana in ɓace in huta, Allah na tuba ka yafe mini kura-kuraina zan cigaba da yin sallah" Ya faɗa yana ɗaga hannu sama alamar addu'a idanunsa suna zubar hawaye. "Allah ka sa in koma kamar ɓera ko ma kiyashi yadda zan ɓuya ba tare da an ga mafaka ta ba" Ya faɗa hawaye suna kwaranyo masa tamkar an buɗe famfo. "Yeeee jama' a ku fito Tajuddin ya dawo sanye da kayan sojoji shikenan mun warke" Cewar Mai Gari da ƙarfi dan ya ga idan ba haka ya yi ba babu wanda zai fito. Ɗif Gwaggo ta yi fuska a cikin dawa. "Ikon Allah na zaune ya faɗi, Taju kuma? Allah sarki Mai Gari kin dai ji yana mini albishir mai daɗi, ya ɗauka ban san na rufe masa ƙofa ba ni kuwa ina sane wai karuwa ta taka matar aure" Ta faɗa a zuciyarta, a take ta yi jifa da fantekar kanta bizigir ta fito daga cikin duron har zaninta yana neman faɗuwa ta kama ta ɗaura. "Kai dai zanin nan nawa kana son a ke ganin tsiraicina, in ba haka ba da yaushe ma na ɗauraka" "Allah sarki ashe dai rai kan ga rai, lallai in da rai da rabo yo ni yanzu ina na ga ta zama wai an ɗaurawa karya zane" Ta faɗa tana fitowa ta buɗe ƙofar ta fito dan sai da ma ta leƙo ta windown ta tabbatar ganin wata dalleliyar fitila. Salele ma bai san ma ya sauke hannuwansa ba, daga ɗaga wa da ya yi yana addu'ar, jin an ce Taju ya dawo. A sukwane ya buɗe ƙofar ya bazamo yana tahowa da sauri har yana tuntuɓehaka ya fito yana haɗa wa da gudu, Kusan a tare suka fito shi da Gwaggo, Malam Mammani ma da ya hango Gwaggo sai ya ji matsalarsa ta zo ƙarshe tun da ga Gwaggo sai su tafi ta karɓi haihuwar amaryarsa Shamsiya. Dan haka shi ma cikin zafin nama ya taho daga turken dabobin da wani jargaggaɓin wandonsa da ya sha fitsari sama da cikin kwando. Fara gudunsa kenan wani ƙaton rago mai manyan ƙaho ya tunguje Malam Mammani sai ga Malam Mammani tamkar iska ta ɗaga leda ya faɗi yashe a wurin ya ji faɗuwar sosai amma sabo da ganin INGOZOMA sai ya yi ta maza ya tashi tsaye ya taho da gudu. Mai Gari ma ganin sun yi ayari kowa ya nufi wajen Taju sai shi ma gudun kar a yi babu shi, amma shi gogan da yake riƙe da fitilar nan ko motsi bai yi ba kamar ma bai san ana yi ba wai kunu a maƙota. "Kai!!!" Matar nan da take tsaye daga gefen Taju ta faɗa da mugun ƙarfi wanda hakan ya sanya su duka suka dakata. Cikin tsananin mamaki Gwaggo ta saki baki dan ita har ga Allah bata lura da matar ba ma, da yake hasken duk ya dalle mata idanu. Su duka huɗun sai yanzu suka yi wa matar kallon nutsuwa, mace ce gabjejiya dan ko za a jaɗe su, su duka huɗun kar in ma za a haɗa har Taju to ba za su kai girman rabin jikinta ba ma. Dan faɗin jikinta tamkar ka haɗa buhun gero biyu ne, girmanta ma ya wuce misali Sai shegen gajarta kamar wata wada. "Taju ka cigaba da aikin ka" Ta faɗa da kakkausar murya, hakan ya sanya su Mai Gari sakin baki kamar layar mai tafiya suna kallonta. Taju kuwa a take ya fara buga ƙafafu yadda sojoji suke yi, ya sara mata kafin daga bisani kuma ya fara fareti yana ta yi yana faɗin "Left right" Tamkar zai ari baki. "Ku in banda ku sakarkaru ne, kuma ma banda sakarci waƙa a tasha haka kuka fito kuna wani gudu tamkar wasu shanaye, shin baku ganni bane? Ko an ce muku bakin rijiya wajan wasan makaho ne? To ku buɗe kunnuwanku ku ji ni, hatta Taju da kuke gani a ƙarƙashin ikona yake dan haka kowa ya iya bakinsa domin bahaushe ya ce iya ruwa fidda kai" Cewar tiƙeƙiyar matar nan cikin wata irin murya mai kama da ta ƴan bariki. "Haba ke kuwa baiwar Allah, yanzu a talatainin daren nan duk da an ce dare mahutar bawa ne amma za ki zo ki nemi ki ɗaga mana hankali, muna cikin tsoron zuwan fatallun ashe dai bonono ne muka yi wai rufin ƙofa da ɓarawo" Gwaggo Ramma ta faɗa tana tafa hannuwa duk da irin dukan luguden da ƙirjinta yake na tsabar tsananin tsoron ƙatuwar matar da tun da uwarta ta haifeta bata taɓa ganin halitta mai girman wannan ba, dan idan akwai wani abu da za a kwatanta da matar to kuwa sai dai a kwatanta ta da giwa, dan tsawo kawai giwa za ta faɗa wa matar. Kuma abin da ya ƙara sanyaya musu jiki irin yadda take ba Taju umarni duk da kayan sojojin da yake jikinsa hakan ne ya sanya suka kasa banbance aya da tsakuwa. "Au Allah har kina da bakin magana to ki sanya a ranki daga yau kun yi ban kwana da zaman lafiya ke hatta dare da rana zai zama ɗaya a wajenku" Matar ta faɗa tana kallonsu. "Haba gingimemiya wai ya haka ne, za ki zo ki yi wani tiƙiƙi da ke kina mana wasu maganganu mararsa kai da ƙaf... Wani mari da ƙatuwar matar nan ta ɗauke Salele da shi, shi ne ya dakatar da shi daga maganar da bai ƙarasa ba. Ƙaran marin ne ya sanya Gwaggo da Mai Gari, juyawa a kiɗime za su koma ɗaki har zanin Gwaggo yana neman faɗuwa ta taro shi. "Duk wanda ya ƙara ɗaga ƙafarsa daga nan sai ya gwammace kiɗa da karatu" Tun kan matar ta ida maganar Gwaggo da Mai Gari suka ja wani uban birki tamkar motar da ta kusa hantsilawa rami ta yi birki. Taju kuwa ganin hukunci da aka yi wa ƙaninsa na mari sai ya bada himma wajen cibaga da faretin da yake yi har ƙara ƙuga "Left right ɗin yake. Salele kuwa marin da aka masa sai da ya ga gilawar taurari masu mugun haske, sannan sai idanun nasa suka yi wani dilim ya daina ganin komai, sai kuma ganinsa ya dawo zafin marin kuwa sai da ya saka shi sakin fitsari a wando. Malam Mammani kuwa a take ya shiga janyo salatin annabi bakinsa banda mismis babu abin da yake dan shi ya tabbatar da shi aka ɗauke da marin to da kuwa idan suma ne ma da ya yi dan yana jin ko zai falka daga suman wataƙila sai ya yi wata bakwai ko sama da haka dan ya ga yanayin jikin matar nan akwai matsala a ce ko lakucin mutum ta yi bare kuma mari. Ɗif gidan ya yi tamkar babu wata halitta a ciki, baka jin komai sai ƙaran faretin Taju da left right da yake faɗa. "Ko akwai mai magana ? Idan akwai ina sauraro dan ni wandon roba nake daidai da ƙugun kowa, duk abin wani zai yi to abin zai zo min a daidai wai mai ido ɗaya ya leƙa kwalba" Ta faɗa tana ƙoƙarin ɗaga ƙafafunta kowa kallonta kawai yake yana mamakin irin ƙibarta, ita kuwa ko a jikinta wai an tsikari kakkausa dan ta san ƙibar nan tata ita ce take ceton ta. Malam Mammani hawaye ya fara na tausayin matarsa ya san ana can ana jiran zuwansa da INGOZOMA amma kuma ga shi daga shi har INGOZOMAR a cikin wani hali. "Taju dakata da aikin nan" Kafin ta rufe bakinta ƙafafun Taju sun tsaya daga faretin, nakinsa ma ya yi ɗif kamar an yi ruwa an ƙafe lunfashinsa ne kaɗai yake aiki a jikinsa dan ya ƙame a waje ɗaya sai hannunsa da ke gefen kunnensa wanda ya sara mata irin yadda sojoji suke sarawa na sama da su. Taju ina so ka faɗa musu wacece ni" "Su ,su, su" "Ka nutsu dalla! Bana son wata in'inna" Ta faɗa tamkar za ta kai masa duka, da sauri ya saita nutsuwarsa ya fara bayani. "Sunan ta yallaɓiya Laila, matar shugaban ƙasar sojojin duniya, tana da ɗa mai suna Nasiru" Ya faɗa yana ƙara daidata nutsuwarsa dan ba ya so ko kaɗan ya yi katoɓara daga bayanin da ta masa abin da zai samu hukunci daga wajenta dan da a ce ta hukunta shi gwara a bashi aikin ƙarfi na sati guda. "Zan zauna da ku na tsawon lukuta ni kaina ban san lokacin tafiyata ba... Dididim diiimmm Gaban Mai Gari Salele, da kuma Gwaggo ya buga jin wai zama za ta yi a gidan bata san ranar tafiyarta ba lallai akwai gwarama. "Taɓɗi! Sha biyun dare marecan kura, ai ni da zuwa gidan nan sai ranar da kika bar gidan nan" Cewar Malam Mammani a ransa yana fatan Allah ya kuɓutar da shi daga gidan. "Ba na son a ke barina da yunwa ko ni ko ɗana, sannan a kowace rana ina cin shinkafa kwano biyar da rana, kai a taƙaice ma a rana ban san iyakacin abin da nake ci ba dan haka a kiyaye, sannan idan lokaci tusa ta ya yi ba na iya yin tusa sai na zauna a kan mutum, sannan tusar take samun damar fitowa, dan haka a duk lokacin da zan yi tusa zan ƙwalawa ɗaya daga cikin ku kira sai ya zo na zauna a kansa na saki tusa ta" Ƙulululuuuuuu, cikin Mai Gari da Gwaggo ya bada, cikin Salele kuwa ya fi na kowa murɗawa saboda ya san yanzun nan matar iya hannu kaɗai ta sa ta mare shi sai da ya gwammace kiɗa da karatu bare kuma a ce ta danne mutum ai sai mutuwa kuma. Malam Mammani kuwa dariyar ƙeta ya fara a zuciyarsa jin wai sai an danne su Mai Gari za a ke yin tusa tabbas ya san za a sha dirama ba ƴar kaɗan ba a gidan. "Allah ya kawo wa jama'ar garin Gumurzu wacce za ta rama musu cuta da cin zalin da Ramma da Mai Gari suke yi" Ya faɗa a ransa yana godewa Allah dan ya san tabbas matar nan sai ta gyara musu zama musamman Mai Gari da ba shi da aiki sai karɓe gonaki da abincin mutane da suka noma kai babu wani abu da Mai Gari ba ya karɓa a hannun mutanensa. MMn Afrah Wtsapp 09013181851 *META FORCE ARZIƘI DAGA ALLAH* ƳAR UWA SHIN BAKI DA LABARIN META FORCE? DA IRIN ƊINBIM ARZIƘIN DA AKE KWASHEWA A CIKINSA, YA AKA YI BAKI YI REGISTER BA? KO BAKI DA BUƘATAR KUƊAƊEN DA ZA KI YI HIDIMAR YAU DA KULLUM? TO KI ZO NI MAMAN AFRAH NA ZO MIKI DA HANYAR SAMUN KUƊI TA WAYAR HANNUNKI KUƊIN YIN REGISTER KAWAI ZA KI TANADA 9K DUBU TARA DOMIN ANA YIN REGISTER DA DALA 5 NE SAI DAI ALLAH KAƊAI YA SAN IRIN RIBAR DA ZA KI SAMU DA KUMA ALKAIRAN DA YAKE CIKIN KASUWANCIN. IDAN KINA SO SHIGA KUMA DA GASKE KIKE KI MINI MAGANA A WANNAN NUMBER 09013181851 IDAN BA YI ZA KI YI BA KAR KI MINI MAGANA DAN BANA SON ƁATA LOKACI! MASU MINI MAGANA KAN HARKAR META FORCE SUNA YIN REGISTER, INA MUKU FATAN ALKAIRI INA TAYA KU MURNA DA SHIGOWA GIDAN ARZIƘI ALLAH SA AN FARA A SA'A🥰 *PROMO PROMO PROMO*💃💃💃💃 Duk wanda zai yi register META FORCE zan cika masa 2k zai kawo 7k maimakon 9k. A hanzarta kar dama ta wuce🥰 [8/19, 17:57] Mom mashkur & Afrah: https://chat.whatsapp.com/EuFGI1TIgdlAhVJXP2XqPJ UNGOZOMA (Mai karɓar haihuwa) NA MAMAN AFRAH F.C.W Ina mata ƴan ƙwalisa, babbar mace alkyabbar mata, macen mai gyara ita wacce ta isa da miji su o'o sai dai su ga ƙeyar mijinta idan ya wuce amma basu ishe shi kallo ba domin babu abin da za su nuna mata. Gyaran gashi babbar martaba ce da take ɗaga darajar mace, musamman kayan gyaran gashin MAMAN ZEE da ya yi fice a ko ina ake labarinsa. Gani ya kori ji sai an gwada akan san na ƙwarai siyan na gari mayar da kuɗi gida💃💃💃💃💃💃💃💃 Hadaddu Kuma ingantattun kayan gyaran gashin mamanzee(chebe hair set) Wadanda suke dawowa da martabar gashin Kai komai lalacewarsa biiznillahi Rabbi Ga kyau ga inganci ga saukin kudi muddin kika fara amfani da kayammu sekindawo Mana da kyakkyawan labari Kanki zeyi kyau ya rika sheki yayi tsayi yayi laushi duk matsalar da ke cikin kanki zata kau in sha Allah Munada set complete Kuma Muna Bada pieces Haka Kuma Muna Bada Sari Muna turawa akowanne gari kike Kuma Ako wacce kasa kike Phone number *08079130166* Page9️⃣➡️🔟 "Ranki shi daɗe jarumar mata, kuma jarumar jarumai mace mai kamar maza kwari ne babu, dan Allah ina neman alfarma a barni in tafi ni ba a gidan nan nake ba dama na zo tafiya da matar gidan ne a kan za ta karɓi haihuwar matata, Allah ya taimaki gimbiya" Malam Mammani ya faɗa cikin tsananin tsoro da karkarwar baki. Kallon tsaf Laila ta shiga masa kafin ta ɗaga ƙafafunta a hankali ta nufi inda yake tsaye. Yadda kika san wata giwa haka take tafiya dakyar sabo da nauyin jikinta. Tun kafin ta ƙaraso gaban Malam Mammani, Malam Mammanin dimm-dimm fitsari ya riga Lailar ƙarasowa. Tana zuwa gabansa ta ja tunga ta tsaya a gabansa Malam Mammani da sauri ya haɗe ƙafafunsa a ƙoƙarinsa na hana kashin da ya ji yana ƙoƙarin zubowa fitowa. Hannu ɗaya ta saka ta kama wuyan rigar Malam Mammani, ta ɗaga shi sama tana riƙe da wuyan rigarsa. Muƙwi ya yi tamkar wani birin da aka tsamo daga ruwan zafi. Tun da ta ɗaga shi bai samu damar sakin ko da numfashi ba haka ya riƙe numfashin na shi gudun kar ya yi numfashin ma ƙaramar magana ta zama babba daga ɗaga shi da wuyan riga kuma sai a yi cilli da shi zuwa saman bishiya. "Ni na baka damar magana? Ko kana so ka ja da ni ne?" "Ni shegiya in ji ɗan daudu wallahi wannan ma da kika ji na yi tsautsayi ne zagin mahaifi, wallahi wautar biri ce har ta sanya shi ganin ayaba tamkar takobi" Ya faɗa yana wani karkata kai tamkar wanda ya yi wani ƙasurgumin laifi. "An faɗa maka ni zaƙin baki yana mini amfani ne, ko an faɗa maka ni ƙaramar danga ce mai daɗin tsallaka?" "Allah huci zuciyarki" Sai da ta jijjiga Malam Mammani sau biyar sannan ta sake shi. "Nasiru!!!" Gabaɗaya wurin saroro suka yi da sakekken baki kamar layar mai tafiya suna jiran su ga wanda aka kira da suna Nasiru, babaram suka ji an bugo ƙofar gidan, da yake ƙofar idan aka buɗe da kanta take koma wa ta rufe, kowa ya sha jinin jikinsa ban da Taju da ya san dama Nasiru ya tsaya a waje. Wani tiƙeƙen yaro ne ya shigo da bai fi shekar biyar ba, sai ƙaton ciki kamar randa, ko kuma mace mai cikin wata bakwai, ga wasu mazaunai kaya guda daga bayansa yana tafiya tamkar saniyar da ta ci ciyawa ta mata karo "Wannan ne ɗana Nasiru da Taju ya muku bayanin ina da ɗa, dan haka ku guji ɓacin ransa, idan kunne ya ji jiki ya tsira. "Mama goyo" Yaron ya faɗa yana zumɓuro baki, da tale ƙafafunsa, Kallon su ta tsaya yi, Gwaggo kuwa kallon bayan Laila ta tsaya yi dan bayan nata kamar faranti yake ko kaɗan babu loko bare a yi batun yin goyo bare ma faɗin bayan nata ya yi yawa. Kallon Gwaggo ta yi wacce tun da Lailar ta juyo gareta gabanta ya yi mummunar faɗuwa dan ta san muddin dai ita ce za ta goyi yaron to kuwa na samu babbar matsala ba ma ƙarama ba. "Ki goya shi, wataƙila bacci yake ji" Muryar Laila ta dawo da Gwaggo daga tunanin da take yi. Babu wani ɓata lokaci Gwaggo ta ruga da gudu ɗaki sai ga ta, ta dawo da zani, a gaban Nasiru ta yi durƙuso kamar mai neman taimako, tiƙi-tiƙi Nasiru ya taka ya haye bayan Gwaggo wacce ta ji tamkar an ɗora mata buhun masara ko na hatsi a bayan. Dakyar ta iya tashi sai nishi take saki kamar wacce ta yi tseren gudun kilomitoci, tun da ta tashi tsaye sai tangal-tangal take tamkar za ta faɗi ta kasa tsayuwa a kan ƙafafunta kwata-kwata domin Nasirun sai rinjayarta yake. "Mene ne hakan wai, ya kike neman jefar da ɗan jiririn yaro?" Laila ta yi maganar cikin tsawa "Ah kin manta mahaifa ƙarewar jariri, yo in ba mahaifa ba ita ce ɗa yake rayuwa a ciki" Cewar Gwaggo a zuciyarta a fili kuma sai ta ce "Ash-sha ɗiyar nan ta yaya zan jefar da shi wallahi tun da na tashi tsayen nan nake ta fama da ƙafafuna a kan su tsaya dangargar amma abin ya faskara sai ja na suke ina ƙwacewa" "Rufewa mutane baki ina abin ma yake wai maye ya ci jariri, wannan har wani nauyi yake da shi da za ki kasa tsayuwa da ƙafarki" "Kai Allah raba bawa da wahala gwauro a teburin mai shayi yau mi Ramma na haɗu da gamona ashe gaba da gabanta aljani ya taka wuta" Gwaggo Ramma ta faɗa a zuciyarta tana tuna irin rashin darajar da take yi wa jama'a amma yau ga shi ido ya juye da mujiya. "Allah baki haƙuri ni ma ai na san yaron nan ba shi da nauyi, ni ma shagwal nake jinsa babu nauyi tamkar ma ban goyi komai ba" Gwaggo ta faɗa tana wani nishi da yake ta faman fitowa ita ma bata san daga inda yake fitowa ba sai dai ta san hakan ba ya rasa nasaba da jibgegen ɗan da ta goya a bayanta sai dai ya ta iya ai faɗan da ya fi ƙarfinka wasa kake mayar da shi. "Ko da na ji" Ta faɗa tana mayar da kallonta kan Mai Gari, Salele da kuma Malam Mammani. "Za ku kwanta a jere rubda ciki zan taka bayan ku wato in yi bene da shi zan wuce" Suka tsinkayi muryar Laila da ta musu dirar mikiya. Su duka sai jikinsu ya fara ƙyarma dan sun tabbata matsawar dai ta taka bayansu to sun kaɗe dan haka Mai Gari cikin sanyin murya ya ce. "Allah ya tamake ki, wallahi wandon nan nawa da kika gani jargaf yake da gudawa, na saki gudawar nan a cikinsa ni kaina ban san adadin kashin da na yi a ciki ba, ko tsayuwar nan ban da wari babu abin da nake yi shi ya sa nake daga baya-baya" Ya faɗa yana fatan Allah sa maganar ta samu shiga. Shiru ta yi kamar ba za ta yi magama ba sai kuma ta ce "Ka tafi ka cire kayan nan yanzun nan kafin warin ya kumbura mutane" Da mugun gudu Mai Gari ya juya ya nufi hanyar bayi ko fitala babu bare takalmi yana ta godewa Allah da ya kuɓutar da shi. Malam Mammani ma ƙarfinsa ya daddage ya ƙwaƙulo kashin ya sake shi a wandon dan shi ma ya tsira daga taka bayansa da shirgegiyar matar nan za ta yi. "Wallahi ni ma hakan take, wandon nan nawa ni ba ma gudawa bane a cikinsa kashi ne mai tauri yana nan musgura-musgura" Ya faɗa a ɗan tsorace dan ba ya so ta ƙara cafkar wuyansa ta ɗaga shi sama irin na ɗazu. Wani mugun kallo ta jefa masa da ya sanya ya sunkuyar da kansa ƙasa. "Ni kuma jinin haila nake in banda ƙarni babu abin da nake, sabo da ban yi ƙunzugu ba(Sanya pad)"Salele da maganar ta fito tamkar an fisgo ta ya faɗa yana tsiltsilla ido Leɓanta na ƙasa ta cije tana saƙa irin abubuwan da za ta shuka a cikin gidan sabo da ta ga abin nasu rainin wayo ne. Malam Mammani da Salele kuwa sai suka ji tamkar su taka rawa dan murna musamman Salele da yake ganin tashi ƙaryar ta take ta kowa dan ya san dai a iya saninsa mata basa haila amna kuma ga shi ana yarda da maganarsa "Ki zunkuɗa shi mana baka ganin goyon kamar bai ji daɗinsa ba" Da sauri Gwaggo ta shiga zunkuɗa Nasiru duk da tana zunkuɗa wa ne dai kwai dan a zunkuɗuwa yake yi ba sabo da yadda gaba ɗaya ya fi ƙarfinta. "Na zunkuɗa shi Ranki ya daɗe, kin san ni ba aikina bane raino shi ya sa ma ban ƙware a goyon ba ɗiya ta ɗaya a duniya kuma ta mutu sai waɗan nan ƴaƴan nata da ta tafi ta barmin su, ni aikina INGOZOMANCI wato karɓar haihuwa, shi ya sa ma kika ji Malam Mammani yana cewa ni ya zo ya kira in karɓi haihuwar matarsa" Gwaggo ta faɗa a ɗan tsrorace tana fatan haƙarta ta cim ma ruwa dan burinta bai wuce Laila ta ce a ajiye goyon ba ta tafi karɓar haihuwar. Shiru Lailar ta yi a ranta tana rayar muguntar da za ta yi wa Gwaggon dan ta lura goyon ne bata so shi ya sa har take ikirarin ba ta iya raino ba. "Ku je da Malam Mammanin ki karɓi haihuwar... "Na gode, na gode sosai " Cewar Gwaggo tana ƙoƙarin sauke Nasiru dan ta tafi, tana jin za ta jefar da ƙwallon mangwaro ta huta da ƙuda. "Idan aka goye shi ba a sauke shi sai dai idan shi ya buƙaci hakan dan haka da shi za ki tafi a bayanki kar ki kuskura ki sauke shi" Ta tsinkayi muryar Laila cikin bada umarni. Wani irin uban zare ido Gwaggo ta yi a ɓoye tana jin tamkar ta kurma ihu dan tana ganin a ce ta tafi har gidan Malam Mammani goye da shirgegen yaron nan ai kuwa tana da jan aiki ja jawur ma kuwa. Gwaggo hatta bakin magana ma rasa wa ta yi Malam Mammani kuwa sai godiya yake zabgawa tamkar ya ari baki dan ya ji hanyar tsora ɗoɗar babu lanƙwasa. "Za ku iya tafiya" "Bari in ɗakko kayan aikin nawa " Gwaggo ta faɗa, tana kama hanyar ɗaki tana tafiya dakyar tamkar an mata dabibayi da igiya ta je ta ɗakko kayanta na karɓar haihuwa. Haka ta fito tana takawa dakyar tamkar raƙumin da aka lodawa kaya, Malam Mammani kuwa gaba ya yi ta bi shi a baya shi yana tafiya zugui-zungui ita kuma tana takawa tinƙis-tinƙis sai wani nishi take tamkar mai naƙudar da take gargarar haihuwa. Malam Mammani sai zabga sauri yake yi dan ya san ya baro matarsa cikin wani hali sannan shi ba dan dole ba, kwata -kwata ba ya so ya kira Gwaggo Ramma karɓar haihuwar matarsa sai dai dan babu yadda zai yi ne, sabo da yadda take bi wajen karɓar haihuwar dan sai an ɗauki mai haihuwa zuwa asibiti ita kuma ba karatun likita ta yi ba amma dan jan magana sai a gado asibiti take karɓar haihuwa bayan suna da masu aikin asibitin nasu wanda suka yi karatu ƴan asalin cikin garin kuma suka samu aiki a asibitin garin amma sabo da mulkin zalunci irin na Mai Gari da Ramma kasa albashin masu aikin asibitin ƙauyen nasu suke a uku su ɗauki kashi ɗai-ɗai, wato idan aka yi albashi dan dole ma'aikatan su kawo albashin su, sai Mai Gari ya raba gida uku shi ɗaya a matsayinsa na Mai Gari sai kuma Gwaggo Ramma a matsayin mai karɓar haihuwa tun da ta hana su, yin aikin su, amma wai sai ana biya ta tun da ita take karɓar haihuwar. "Alla ka fitar da A'i daga rogo, Allah sa yadda Ramma take a birkice kar ta ce sai an kai Shamsiya asibiti ta yarda ta karɓi haihuwar a gida" Cewar Malam Mammani a zuciyarsa. Yana mai waiwaya wa bayansa amma sai ya hango Gwaggo a can bayan tana tafiya a ɗan sunkuye kamar mai ƙusumbin Sai da ya dangana da ƙofar gidansa ya samu ya tsaya domin jiran Gwaggon ta ƙara so, yana nan tsaye sai ga ta, ta ƙara so bakinta buɗe tana ta sakin numfashi ta bakin dan zuwa lokacin Nasiru ya yi bacci a bayan nata, ga wani warin kashin Malam Mammani da ya cika mata hanci, duk da kashin nasa ya faɗi a hanya ta ƙafar wandon. "Wash Allah na, da a ce in yi goyon nan gwara a ce a ɗora mini buhun hatsi a ganina sai na fi jin rashin nauyinsa" Cewar Gwaggo lokacin da ta ƙaraso ta kama jikin bishiya ta riƙe tamkar mai haihuwar da kan ɗa ke ƙoƙarin fitowa. " A yi haƙuri dai Ramma, mai kika ce gwara buhun hatsi?" "Abin da wancan ya ce shi na ce kirarin mai tsoro" Gwaggo ta faɗa tana aikawa Malam Mammani harara. "Allah baki haƙuri ba ni na kai zomon ba rataya aka ba ni" Ya faɗa a zuciyarsa. "Ramma in samo amalanken shanu a kai Talatuwar asibitin ne?" "Haba Malam Mammani in banda dai rashin imani cirewa kare hanta da ransa ta yaya zan iya zuwa wani asibiti da wannan goyon to aradu sai dai in tafi da rarrafe dan na yi imani da Allah babu mai machine ɗin da zai iya ɗaukana da goyon ɗan nan, ko amalanken shanun na hau na san sai taya ta sace, ko ma shanun su kasa tafiya amalanken take ƙiƙar-ƙiƙar" "Alhamdulillah! Ni kamar dan ni tsintuwar haƙorin makka a hasken farin wata" Cewar Malam Mammani a ransa. A hankali Gwaggo ta juya ta shiga gidan tana ɗaga ƙafa dakyar Haka ya bi bayanta, matan gidan suna jin sallamar mai gidan suka fara shigewa ɗaki suna rufowa da yake matansa huɗu Shamsiyya ita ce amarya kuma ita ce yarinya ba ta fi ƴar cikinsa ba ko ma jika. Kowacce tana leƙowa daga window sabo da tsegumi dan tun da suka Talatuwar tana naƙuda kowacce ta ƙi kwanta wa a cewar su sai sun ga ƙwal uwar daka. Malam Mammani kuwa turakarsa ya wuce ya tsafta ce jikinsa ya canja kaya ya dawo lokacin Gwaggo tana durƙushe a gaban Talatuwaa da take ta rafka ihu da kakarta da take ta miƙa mata wani ruwan rubutu a kofi. "Kar ki kuskura ki bata rubutun naƙuda, idan kuwa kika aikata haka ki sani tabbas kin aikata babban kuskuren da ba za taɓa gyaruwa ba" Gwaggo ta faɗa cikin bada umarni tana sakin nishi tamkar ita ce mai naƙudar sabo da goyon da yake bayanta. Karkarwa hannun matar ya shiga yi dan ta san dama ba a neman wani abu da ya shafi haihuwa a wajen kowa sai dai wajen Gwaggo Ramma. Haka Gwaggon ta saka hannu duk da nauyin goyon bayanta, ta sakarwa Talatuwa duka a baya wai sabo da rakin da take yi, ƙaran dukan sai da ya sanya Kakar Talatuwa zabura ta dafe haɓa ganin an daki wacce take cikin halin naƙuda amma sai dai babu yadda za ta yi dan ta san tana yin magana cibi zai zama ƙari. Dama haka Gwaggo take Ungozomanci kafin ta gama karɓar haihuwa mai naƙuda ta ci uban dukaTalatuwa kuwa sai ta ji tamkar an ƙara mata ciwon ne amma haka ta daure ta danne ta yi shiru take salati a zuciyarta. Gwagggo ko a jikinta wai an tsikari kakkausa, cikin rashin tausayi ta saka hannu wai za ta gyara kan ɗan da ya ƙi gaba ya ƙi baya. Tana saka hannun sai ta ji hannun jariri ya damƙi hannunta, cikin tsantsar mamaki take ƙoƙarin ciro hannunta amma abin sai ya gagari kwandila, jin hannun yaro ya mata riƙon da ko ƙaton hannun ba za ta iya ba. "To mai yake faruwa da ni ne?" Gwaggo ta jefawa kanta tambayar a zuciyarta amma tsoro fal ranta dan yanzu tana fuskantar matsaloli a wajen aiwatar da aikinta na UNGOZOMA. "Kai shegen jariri sakar mini hannu tun da tun kan uwaka ta bayyana a duniya hannun yake a duniyar" Gwaggo ta faɗa a fili tana yaƙi da kuɓuto da hannunta. Kakar Talatuwa sai ta bi Gwaggo da kallon mamaki ganin tana ta janyo hannunta amma kamar ma hannun ƙara yin ciki yake yi, kafin Kakar Talatuwar ta samu zarafin yin magana sai kawai suka ga wuri ya fara komawa yana matsewa tamkar dai ba shi ne ya buɗe ba sabo da fitowar ɗa amma yanzu sai ya koma kamar ba haihuwa Shamsiyyar za ta yi ba, sai wuri ya koma ya rufe ruf amma da hannun Gwaggon a ciki. "Keeee! Ɗiyar nan tashi maza aljani ne a cikin ki ba ɗan mutum bane ya kama hannuna ya riƙe ku taimakeni ku kawo ɗauki kar na zama mai hannu ɗaya a garin karɓar haihuwa" Cewar Inna da gumi ya gama jiƙa ta jargaf idanu sun raina fata sai zare su take tamar an kama kwarto a ɗakin amarya, ga wannan goyo na Nasiru da bata sauke ba sabo da Laila da ta ce ba a sauke shi. Talatuwa kwa da take kwance ta buɗe ƙafafu a take gabanta ya bada wani dududuuummmmmm! Masu biyo ni pc a kan a saka su grp ga link nan. Wanda suke tambayar litattafaina na abin dariya akwai cmplt kowanne doc 500 ƳAR ZAMAN WANKA ƘARA'IN INNA DELU JALLI JOGA. MAMAN AFRAH Whatsapp 09013181851 *META FORCE ARZIƘI DAGA ALLAH* ƳAR UWA SHIN BAKI DA LABARIN META FORCE? DA IRIN ƊINBIM ARZIƘIN DA AKE KWASHEWA A CIKINSA, YA AKA YI BAKI YI REGISTER BA? KO BAKI DA BUƘATAR KUƊAƊEN DA ZA KI YI HIDIMAR YAU DA KULLUM? TO KI ZO NI MAMAN AFRAH NA ZO MIKI DA HANYAR SAMUN KUƊI TA WAYAR HANNUNKI KUƊIN YIN REGISTER KAWAI ZA KI TANADA 9K DUBU TARA DOMIN ANA YIN REGISTER DA DALA 5 NE SAI DAI ALLAH KAƊAI YA SAN IRIN RIBAR DA ZA KI SAMU DA KUMA ALKAIRAN DA YAKE CIKIN KASUWANCIN. IDAN KINA SO SHIGA KUMA DA GASKE KIKE KI MINI MAGANA A WANNAN NUMBER 09013181851 IDAN BA YI ZA KI YI BA KAR KI MINI MAGANA DAN BANA SON ƁATA LOKACI! [8/19, 17:57] Mom mashkur & Afrah: UNGOZOMA (Mai karɓar haihuwa) NA MAMAN AFRAH F.C.W GARGAƊI⚠️ Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ta kowace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowace kafa ba sai da izinina a kiyaye. Ina mata ƴan ƙwalisa, babbar mace alkyabbar mata, macen mai gyara ita wacce ta isa da miji su o'o sai dai su ga ƙeyar mijinta idan ya wuce amma basu ishe shi kallo ba domin babu abin da za su nuna mata. Gyaran gashi babbar martaba ce da take ɗaga darajar mace, musamman kayan gyaran gashin MAMAN ZEE da ya yi fice a ko ina ake labarinsa. Gani ya kori ji sai an gwada akan san na ƙwarai siyan na gari mayar da kuɗi gida💃💃💃💃💃💃💃💃 Hadaddu Kuma ingantattun kayan gyaran gashin mamanzee(chebe hair set) Wadanda suke dawowa da martabar gashin Kai komai lalacewarsa biiznillahi Rabbi Ga kyau ga inganci ga saukin kudi muddin kika fara amfani da kayammu sekindawo Mana da kyakkyawan labari Kanki zeyi kyau ya rika sheki yayi tsayi yayi laushi duk matsalar da ke cikin kanki zata kau in sha Allah Munada set complete Kuma Muna Bada pieces Haka Kuma Muna Bada Sari Muna turawa akowanne gari kike Kuma Ako wacce kasa kike Phone number *08079130166* Page 1️⃣1️⃣➡️1️⃣2️⃣ *GIDAN MAI GARI* Tun da su Gwaggo suka fita, Laila ba ta matsa daga inda take ba, tana nan a tsaye har Mai Gari ya canja kaya, haka ma Salele, shi kuma Taju umarni ta ba shi ya fita ya ɗakko akwatin kayanta da ta sanya ya ajiye a waje, domin tun da suka je gidan Mai Gari tsohon inda ya taso sai wasu samari da suke tsaye a wajen kamar dai ma ƴan shaye-shaye ne suka iyo dare daga yawonsu suka sanar musu inda ya koma suka musu kwatance hakan ya sanya basu yi ƙasa a gwiwa ba suka ɗunguma zuwa sabon gidan da suka koma ɗin. Mai Gari kai tsaye ya shiga ɗaki yana ƙoƙarin turo ƙofa Laila ta rangaɗa masa kira mai kama da na ƴan farauta wanda sai da hantar cikinsa ta kaɗa. Cikin son cika umarninta ya taho dan ya san dai bahaushe yana cewa in ka ji kira samu ne amma ban da kiran ɗan sanda, to yanzu ma dai ya san wannan kiran matar mai kama da butar shayi kan gajarta kiranta ba zai taɓa zama alkairi ba. Tun da ya zo ba ta ce masa komai ba dan haka da ya tsaya sai ya ja bakinsa ya rufe yana jiran umarni daga gareta a hakan ne ya ɗan kalli Taju da yake daga bayanta yana riƙe da akwati kuma ya ƙame a wuri ɗaya, alama Taju ya masa a kan ya durƙusa aikuwa cikin sauri Mai Gari ya duƙa tamkar mai neman yafiya. "Kai! Mai jinin haila (Priod) Idan ka yi ƙunzugun ina son ganinka a nan" Ta faɗa daidai lokacin da Salele ya durfafi ɗaki zai shiga bayan ya fito daga bayi wanda can ya je da kayansa ya tsaftace jikinsa daga fitsarin da ya sha shararawa ya sako kayansa ransa fal murna ya tsira daga hannun masifaffiyar matar nan amma kuma kiran da ta masa ya sa ya sha jinin jikinsa. Da har hannu ya kai ya taɓo hantsar wandonsa jin ta ce idan ya gama ƙunzugun. Cikin sanyin jiki ya taho yana zuwa shi ma sai ya je kusa da Kakan nasa ya durƙusa kamar yadda Kakan na shi ya yi sai suka yi layi tamkar wasu almajirai. "Ina so cikin sauri ku gyara mini ɗakin da zan zauna, dan haka duk wani tarkace ku kwashe daga wancan ɗakin, ku mayar wancan inda za ku kwatsu a ciki ni kuma in zauna a wancan ɗin" Ta faɗa tana musu nuni da ɗakin Gwago, kallon kallo aka fara tsakanin Salele da Mai Gari, Taju kwa da dama ya san a rina wai an saci zanen mahaukaciya babu abin da ya furta sai ma danne dariyarsa da yake sabo da yadda ya hangi idanun Mai Gari sai micincina su yake bakin nan nashi a hangame kamar ƙofar gari tsabar mamaki sai dai babu damar yin musu, dan da a ce wani ne ya nemi shigarwa Mai Garin hanci da ƙudundune da tuni ya yi maganinsa nan take amma yadda matar nan take jibgaga tabbas ko a hamatar ta, ta saka shi ta matse zai iya garzayawa barzahu ya rasa ma dalilin da ya sa yake jin wani mugun tsoranta. "Tabbas matar nan na ga alama hatta shugabancin nawa na Mai Gari da nake tattalawa nema take ta saka ƙafa ta yi fatali da shi wallahi ba dan Allah ya yi ta gansamemiyar nan ba da babu abin da ta isa ta yi iko da ni in yi" Mai Gari ya faɗa a zuciyarsa yana sauke idanunsa a kan dantsen hannun Laila da yake ganin kaurin dantsen tamkar jikin ƙatuwar bishiyar ayaba, sai dai gashin kanta da ya zubo har kan kafaɗarta wanda dare bai hana shi yin sheƙi ba kana ganinsa ka san yana samun gyara da kayan gyaran kai a MAMAN ZEE (Chebe hair set) Wadanda suke dawowa da martabar gashin Kai komai lalacewarsa biiznillahi Rabbi Ga kyau ga inganci ga saukin kudi muddin kika fara amfani da kayammu sekindawo Mana da kyakkyawan labari Kanki zeyi kyau ya rika sheki yayi tsayi yayi laushi duk matsalar da ke cikin kanki zata kau in sha Allah Munada set complete Kuma Muna Bada pieces Haka Kuma Muna Bada Sari Muna turawa akowanne gari kike Kuma Ako wacce kasa kike Phone number *08079130166* "To, to, to, Ranki shi daɗe bari a yi yadda kika ce" Ya faɗa a ladabce yana tashi shi ma Salele tashin ya yi, Mai Gari ya juya Salele ya take masa baya, Taju ma bin bayan nasu ya yi ɗauke da akwatin ita kuma ta kame a wajen ba tare da ta motsa ba. Suna shiga ɗaki Salele cikin raɗa har yana doɓara bakinsa a kunnen Mai Gari ya ce "Wannan mata an yi shegiya wallahi yanzu Mai Gari kana ji da gani za ka bari mu kwatsu ɗaki ɗaya ina matsayin naka na Mai Gari? Za a mayar da kai sahun gwaurayen samari" "Kai dalla rufe mini baki sakaran wofi, wannan matar mai halitta jiki duk a murɗe kamar ƴar dambe haka kawai in mata musu in baƙunci lahira ko in kwanta jinya a banza to wallahi gwara ko a turken dabobi ta mini matsugunni in ke kwanciya daga duniyar sai ina?" Mai Gari ya faɗa cikin raɗar shi ma yana aika wa Salele harara, ɗif Salelen ya yi haka suka kwashe tarkacen ɗakin hatta kayan Gwaggo babu abin da suka bari suka share ɗakin tatas. Sun gama sai Taju ya shigo ɗakin da akwatin a hannunsa dan dama a baranda ya tsaya yana ajiyewa ya juya da sauri zai fita ai kuwa Mai Gari ya saka hannu ya damƙo shi ya dawo da shi cikin ɗakin cikin ƙasa da murya ya ce "Kai ɗan nema a gidan uban wa ka samo wannan matar mai kamar an laulaya tayota abu unguwa guda ko kyan gani babu haka kawai ka kwaso jaraba ka shigo mana da ita gida ana zaune ƙalaw kuma ma, sabo da kun mayar da mu sha ka tafi a ce wai matar shugaban ƙasar sojoji, sai ka ce wanda ba mu da hankali? in ce dai shugaban ƙasa ɗaya ake yi a ƙasa amma sabo da rainin hankali a ce mana wai shugaban ƙasar ma har da na sojoji" Tun da ya fara maganar Taju yake masa nuni da ya yi shiru duk da cikin raɗa yake maganar amma dai ya fi so ya bar maganar dan shi ya san halin Laila kunnuwanta kamar na miciji suke. "Kai dallah ragwan maza rufe mini baki sai wani mismis kake da baki kamar sabon baƙon munafuki, ga kayan sojoji a jikin ka amma ka kasa kataɓus ka tsaya mace tana juya ka kamar waina a tanda ka ɗakko annoba ka... "Taju" Kiran da Laila ta yi wa Taju wanda hakan yake nuni da ta matso ƙofar ɗakin dan a dab da ɗakin suka tsinkayi muryarta, hakan ya sanya Taju ya fisge riƙon da Mai Gari ya masa cikin sauri, Mai Gari kuwa wani irin faɗuwa gabansa ya yi, juyawa ya yi ya kalli gabas yana faman rattabo addu'a a zuciyarsa a kan Allah masa tsari da sharrin Laila dan shi tunaninsa Laila ta ji abin da yake faɗa. Bayan ya gama addu'ar a ransa sai kuma ya ɗaga hannunsa ya sauke wa fuskarsa tagwayen maruka guda biyu, a kan idanun Laila ya mari kansa lokacin ta leƙo ɗakin dan ganin wainar da suka toya. Idanu ta sauke a kan Mai Gari da ya koma jikin bango ya raɓe yana murza fuskarsa dan ya maru sosai dan da ƙarfi ya mari kan nasa, dan ma kar ya yi a hankali ta ce za ta sake masa wani shi kuma da a ce ta mare shi da wannan hannun nata gwara ya mari kansa ko da sau goma ne kuwa. "Na yi wa kaina hisabi ma ba sai kin mini ba" Ya faɗa yana karkarwar baki. "Taɓ rikicin duniya da mai rai ake, wai yau Mai Gari ne haka ya faɗo ƙasa warwas, mutumin da babu wanda ya isa ya taka shi sai baƙin mulkin tsiya da cin zali amma yau ga shi Allah ya kawo mai yin maganinsa har gida kuma cikin ruwan sanyi" Salele ya faɗa a zuciyarsa. "To ai ni babu abin da ka mini hisabin mai kuma?" Ta faɗa tana nishi tamkar wacce ta yi tseran gudu sabo da tafiyar da ta yi daga tsakar gida zuwa ɗakin Gwaggo. "Oh duniya makaranta wallahi da na san baki ji maganar da nake faɗa wa Taju ba da babu abin da zai sa in mari kaina maruka ƙwarara guda biyu ashe dai gudun gara na yi na tarar da zago, ni da na mari kaina sabo da kar ki mini irin marin da kika yi wa Salele mari mai kama da an mari mutum da faskare" Cewar Mai Gari a zuciyarsa a fili kuma cikin ɗacin zuciya ya shiga faɗin. "Ah dama fa na ɗauka ko gyaran ɗakin ne bai yi ba" Banza ta masa kamar ma ba ta ji abin da ya ce ba. "Ku fita ku bani waje" Ta faɗa tamkar wadda ta ke korar dabobi. "Oh da'ira cuta bayan rai, kai da gidanka amma ake maka korar kare ana maka iko, duk da ba mallakina bane gidan amma dai ai ni ne a ciki, amma sai a ke mini hawan ƙawara" Mai Gari ya faɗa a zuciyarsa har suna rige-rigen fita shi da Salele ban da Taju da yake gefe a tsaye yana jiran abin da za ta ce. "Fita ka bani waje kai ɗin ma zan yi bacci" "An gama" Ya faɗa a ransa yana juyawa ya fita har da ja mata ƙofar dan ƙarfin hali. Yana fitowa ya saki wata ajiyar zuciya tamkar wanda ya kuɓuto daga bakin kura. Ɗakin da su Mai Gari suka shiga ya kutsa kai ciki ya same su sun haɗa kai suna magana ƙusƙus. Yana shigowa Salele ya tashi ya fita sai da ya ƙarewa ƙofar ɗakin da Laila take kallo ya tabbatar ba ta wajen ya dawo ya kara ƙofar ɗakin yana shirin saka sakata Taju ya ce "Kar ka saka sakata ka bar ƙofar a haka dan wannan komai dare kira take kuma daga ta yi kiran dole mutum ya amsa kiran nata, kamar dai kiran mutuwa" "Sai ka ce gidan mahaukata, to ai ko a gidan kaso ma ana bacci domin shi dare mahutar bawa ne" Mai Gari ya faɗa yana hayayyaƙowa Taju dan yana ganin duk shi ya saka su a cikin wannan masifar da suke ciki. Salele dai bai saka sakatar ba ya bar ƙofar a kare dan ba ya so a ce shi ne da laifin rufe ƙofa dan ba ya so ko a mafarki Laila ta ƙara marinsa bare a zahiri. Dan ya lura al'amuranta hajaran majaran ne shiga aljannar alƙali. Bayan sun yi tsit tamkar ruwa ya ci su, Mai Gari ya yi gyaran murya ya fara magana cikin raɗa -raɗa dan su duka ukun suna waje ɗaya sun haɗa kai kamar masu neman gafara dan ko ƙwaƙƙwaran motsi ba sa yi sabo da tsananin taka tsan-tsan. "Wai ni kai Taju ban da rashin hankali kamar renon gwauro, haka kawai ka ɗakko matar nan mai ƙirar samudawa ka kawo mana jaraba gida, kana ganina fuskata kamar ta tsulan biri, ita kuma Kakar ka Ramma kana ganinta caca kurukuci cikon benci, haka kawai ka kawo mana abin da zai kashe mu murus kamar wutar da aka zubawa ruwa" "Mai Gari ka manta baka ce masa ni jikina akwai ya babu ba ne kakar wajen uba" Salele ya faɗa shi ma cikin raɗar dan su duka sun haɗa fuskoki a waje ɗaya kuma yanzu a duhu suke dan sun kashe haske sai na farin wata fitilar Laila kuwa Taju ya bar mata. "Na ce a ina ka samo matar nan baƙar fura ana gama ki mai gida yana mutuwa?" Mai Gari ya tambaye sa cikin raɗar dai. "Ana tsoronka ɗan mayya, ya ce daga ni har uwata" Cewar Taju a zuciyarsa yana jin tamkar ya fashe da dariya dan yana hango yadda bakin Mai Gari yake raɗa ta hasken farin watan da ya shigo kuma yadda yake yi ɗin muryarsa har wani shaƙe ta yake shi ala dole kar Laila ta jiyo abin da yake faɗa duk da ba a ɗaki ɗaya suke ba sai dai hanyar lafiya ce ake bin ta da shekara. A fili kuma sai ya ce "Mai Gari na faɗa maka matar shugaban ƙasar sojoji ce" "Gwafar ubanka, na ce gwafar ubanka kai da ƙasar lanjeriyar (Nigeri'a) Da shugan ƙasar sojojin... "A'a Mai Gari da alheri uwar kishiya ta hau kura,ka san dai kwarankwatsa dubu matar nan ta ji wannan maganar sai ta maka yadda ta yi wa Malam Mammani da ta ɗaga shi sama kamar jemage, kasan farilla tusa a masallaci sai ta maka abin da ya fi hakan" Salele ma ya katse Mai Gari cikin ta shi raɗar. Shiru Mai Gari ya yi tare da haɗiye wani yawu mudukkk dan bai manta irin yadda ta ɗaga Malam Mammani ba kamar wanda ta ɗaga jaririn kyankyaso. "Haka ne kuma kaima da gaskiyarka Salele tabbas a lokacin da mage take wuri ɓera ba ya sata amma kuma an dake ni a hana ni kuka, duk da dai gwara ya ba ni amsar tambayata tun da a gama yau ya fi a ƙarasa gobe, amma dai da na ɗauka da zafi dan cewa zan yi a yi abin da za a yi mahaukaci ya ɗauki rigar kurma" "Mai Gari ni fa gaskiya nake faɗa maka" Taju ya faɗa a fili a zuciyarsa kuma ya ce "Sai dai ku yi haƙuri domin kuwa ni ma ba da son raina ba, babu wata matar shugaban ƙasar sojoji wallahi dadirona ce, ta gidan karuwai haka kawai tun da na haɗu da ita take tatsa ta kamar ta samu nonon saniya, duk wani kuɗi da zan samu ita take ƙwacewa, duk inda na je sai ta bi ni, kuma ni babu aikin sojan da na samu wannan kayan ma a wajen ƴan wanki da guga na sato su a kan igiyar shanya, shi ne na ɓoye dan idan na dawo nan garin in ke yankar mutane da su, ina ƙaryar ni soja ne amma tun da na tafi neman kuɗi nake irin su dako da dai sauran aikin neman kuɗi, yau da na shirya zan taho gida har hula na saka na rufe fuskata dan kar wani ya faɗa wa Laila zan gudu amma abin mamaki, da na shiga motar haya sai da muka yi nisa na gane ashe tana ma cikin motar, har da ɗanta ɗan gaba da fatiha (Wanda aka haifa babu aure) Ana sauke ni ta sauka, shi ne ta saka na saka kayan nan na sojoji muka shigo garin nan tun a hanya ta shinfiɗa mini dokoki ni kaina ban san ranar da za ta bar garin nan ba, kuma kona can ba na mata musu dan ina yin musu sai ta gana mini azaba da ƙibar jikinta, a shegen son manyan matana wanda ake yi wa laƙabi da matan manya, wani abokina ya ce in je wani ɗaki ya tanadar mini irin matar da nake so ina zuwa na yi arba da ita ta yi gandaƙaiƙai, a kiɗime na juya zan gudu ta janyo ni ta dawo da ni ɗakin, tun daga wannan ranar ban sake samun kwanciyar hankali ba duk ta bi ta tatiƙe ni, ko kaina ba na yi wa amfanin da nake mata " Ya faɗa yana jin ƙwallar tausayin kansa tana ciko masa idanu yana jin da na sani a kan neman matan banza tun da ga shi ta dalilin hakan ya gamu da gamonsa. "To ni dai wallahi ban yarda ba, mene ne haɗina da soja dama kai ne ka tafi aikin kuma shekara guda baka dawo ba, bare ko albarkacin aikin naka mu ci, sai yanzu za ka dawo da wacce za ta kassara ni, ta nakasta mu, yo ciyar da wannan matar ai ba ƙaramin aiki bane" Cewar Mai Gari cikin ɓacin rai har maganar ta shi tana fitowa ya manta cewar raɗa suke, da sauri Salele ya saka hannu ya rufewa Mai Gari baki dan shi ba ya son abin da zai sa ya sake samun mari daga Laila da wannan hannun nata mai kamar na kantoma. "Kai ni barni in faɗa in banda hankalinsa a kan hanci yake ba a ƙwaƙwalwarsa ba, ta yaya zai kawo mana wannan abin gida wannan ai abin banza ne hanci ba ƙafa" Cewar Mai Gari da ya janye hannun Salele daga kan bakinsa rai a ɓace yake magana. "Wallahi Mai Gari abin daga Allah yake matar mai takaba ta yi ciki, kuma gani ma na yi abin duniya mene ne dan kaza ta jawo muzuru kwanan gida... "Taju!!!" Ƙaran kiran da Laila ta ƙwala masa shi ne ya dakatar da shi daga maganar da yake yi. A kiɗime su duka ukun suka kwanta a wajen da suke zaune sai ya zamana gabaɗaya kawunansu a haɗe a waje ɗaya ma'ana sun yi murhu. "Kai dan matar ubanka da bai aura ba, ka tashi ka tafi kiran wannan" Mai Gari ya faɗa daga kwancen da yake. "Ai wallahi ka tafi kar ka janyo mana" Salele ya faɗa yana zungurin ƙafar Taju. "Ku baku san kiran da take yi bane, wallahi na san ko rantsuwa na yi ba zan yi kaffara ba, tusa ce ta matso ta, kuma kun san ita idan za ta yi tusa dole sai ta zauna a kan mutum, dan in har za ta yi tusa ba tare da ta zauna a kf mutum ba to mazaunanta tsagewa suke saboda yadda tusar ta take fitowa a guje da mugun ƙarfi shi ya sa sai ta zauna a kan mutum ta murtsuka mazaunanta sai ta saki tusar hakan shi ne zaman lafiyar ta" Taju ya faɗa a hankali yana sakin wani marayan kuka dan ya san akwai babbar matsala. Maman Afrah Whatsapp 09013181851 *META FORCE ARZIƘI DAGA ALLAH* ƳAR UWA SHIN BAKI DA LABARIN META FORCE? DA IRIN ƊINBIM ARZIƘIN DA AKE KWASHEWA A CIKINSA, YA AKA YI BAKI YI REGISTER BA? KO BAKI DA BUƘATAR KUƊAƊEN DA ZA KI YI HIDIMAR YAU DA KULLUM? TO KI ZO NI MAMAN AFRAH NA ZO MIKI DA HANYAR SAMUN KUƊI TA WAYAR HANNUNKI KUƊIN YIN REGISTER KAWAI ZA KI TANADA 9K DUBU TARA DOMIN ANA YIN REGISTER DA DALA 5 NE SAI DAI ALLAH KAƊAI YA SAN IRIN RIBAR DA ZA KI SAMU DA KUMA ALKAIRAN DA YAKE CIKIN KASUWANCIN. IDAN KINA SO SHIGA KUMA DA GASKE KIKE KI MINI MAGANA A WANNAN NUMBER 09013181851 IDAN BA YI ZA KI YI BA KAR KI MINI MAGANA DAN BANA SON ƁATA LOKACI! AKWAI CIKON 2K GA WANDA ZAI YI REGISTER META FORCE ZAI KAWO 7K MAIMAKON 9K KAR KU BARI DAMA TA WUCE KU KI MINI MAGANA A 09013181851 DOMIN A DAMA HARKAR ARZIƘI DA KE, KINA ZAUNE BABU SANA,A GA DAMA TA SAMU DA WAYARKI TA HANNU ZA KI MALLAKI KUƊAƊE😍 [8/19, 17:57] Mom mashkur & Afrah: UNGOZOMA (Mai karɓar haihuwa) NA MAMAN AFRAH FCW GARGAƊI⚠️ Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ta kowace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowace kafa ba sai da izinina a kiyaye. Ina mata ƴan ƙwalisa, babbar mace alkyabbar mata, macen mai gyara ita wacce ta isa da miji su o'o sai dai su ga ƙeyar mijinta idan ya wuce amma basu ishe shi kallo ba domin babu abin da za su nuna mata. Gyaran gashi babbar martaba ce da take ɗaga darajar mace, musamman kayan gyaran gashin MAMAN ZEE da ya yi fice a ko ina ake labarinsa. Gani ya kori ji sai an gwada akan san na ƙwarai siyan na gari mayar da kuɗi gida💃💃💃💃💃💃💃💃 Hadaddu Kuma ingantattun kayan gyaran gashin mamanzee(chebe hair set) Wadanda suke dawowa da martabar gashin Kai komai lalacewarsa biiznillahi Rabbi Ga kyau ga inganci ga saukin kudi muddin kika fara amfani da kayammu sekindawo Mana da kyakkyawan labari Kanki zeyi kyau ya rika sheki yayi tsayi yayi laushi duk matsalar da ke cikin kanki zata kau in sha Allah Munada set complete Kuma Muna Bada pieces Haka Kuma Muna Bada Sari Muna turawa akowanne gari kike Kuma Ako wacce kasa kike Phone number *08079130166* Page 1️⃣3️⃣➡️1️⃣4️⃣ *GWAGGO RAMMA* Jin ana lallanƙwasa mata yatsunta daga ciki ya sa ta fara karanto addu'ar da duk ta samu nasarar wartowa a bakinta, domin kuwa tun da ta fara sana'ar nan ta UNGOZOMANCI ba ta taɓa tsintar kanta a wannan yanayi ba haƙiƙa wannan baƙon abu ne a gare ta. "Ni Ramma yau na ga dalili mai sa a leƙa gaban sirika, lallai na yankowa kaina kazar wahalar da ban san ma ta inda zan fara fige ta ba" Ta faɗa a zuciyarta a fili kuma sai ta ce "Baiwar Allah taimake ni mana kina ganin mafitar ɗa (HQ) Ya rufe da hannuna a ciki, kar fa a je hannun nawa ya shige cikin mahaifar in shiga uku, kuma wallahi ɗan nan ba jariri bane dan ina jin daga ciki sai lanƙwasa mini yatsu yake tamkar ya samu machine ɗin matsa ruga" Ta faɗa cikin sanyin murya tana wani nishi nauyin goyon Nasiru da ta ji gaba ɗaya ya sanya bayanta ya yi sagewar da take jin lallai sai ta nemi maganin ciwon jiki ko ta samu salama. Duk da Kakar Shamsiyya tana cikin tashin hankalin ganin jariri ya koma ƙofar kuma ta rufe ruf da hannun UNGOZOMA a ciki amma kuma ba ta manta da abin da Gwaggo Rammar ta mata ba dan haka sai ta kawar da kanta gefe. "Kaka dan Allah ki taimaka kar ɗan nan ya sha ruwan naƙuda " Talatuwa ta faɗa cikin sanyin muryar dan gaba ɗaya ta sare da lamarin dan ita ma tana jin tamkar wanda ake yaƙin badar a ƙasan nata, wani lokacin ma sai ta ji tamkar wanda jaririn yake rawa ko tsalle a ciki wannan ne al'amarin da ya ƙara ɗaga mata hankali da ta fara tunanin kar dai ba ɗan mutum bane a cikin nata kamar yadda ta ji Gwaggo Ramma ta faɗa. "Kaka magana nake fa" Ta ƙara faɗa ganin kakar tata ba ta furta komai ba. "Haba Shamsiyya ina abin ma yake wai maye ya ci ɗan jinjiri, duk abin nan da kika gani ina sane wai karuwa ta taka matar aure, ai kowa ya yi nagari kansa, ki bari mu ga iya gudun ruwan UNGOZOMA tukunna ta faɗa tana kallon Gwaggo da take ta faman sharɓar gumi yankar ita ce take naƙudar, tun da a haifi ɗa da samu ya fi a mutu a bar masa gado" "Ki taimaka baiwar Allah, duk wanda ya taimaki wani Allah zai taimake shi kuma ai faɗan da ya fi ƙarfinka wasa kake mayar da shi... Maganar Gwaggo ce ta yanke ganin Talatuwar tana wani irin mimmiƙewa, cikin tashin hankali kamar ta kama ta ta rirriƙe ta tana jijjiga ta. "Ashshahadu an la'ilaha illlallahu wa ashshadu anna muhammadur rasulullahi" Cewar Gwaggo cikin ɗaga murya tana sakin wani kuka jin Talatuwar tana kalmar shahada. "Dole ne ni ma in yi salatin nan, kar ki cika da kalmar shahada ki bar ni, in cika da hayagagar wofi dan na san ni da ke mutuwar kasko za mu yi tun da ga shi hannuna yana maƙale a jikin ki, to kuwa kina mutuwa na san tare za a haɗa mu a kabari ɗaya" Gwaggo ta faɗa tana sakin wani marayan kuka da ya sanya gaba ɗaya mutanen gidan suka jiyo ta. Kakar ma kuka ta fasa mai wani irin ƙara, ganin jikin Talatuwar ya saki gaba ɗaya alamar ta daina numfashi. "Shikenan ta faru ta ƙare an yi wa mai dami ɗaya sata, ni ma mutuwar zan yi yanzu, ni ma wallahi ba zan tafi ni kaɗai ba " Gwaggo ta faɗa tana kai hannun nata ɗaya ta danne Nasiru da yake bayanta ita ala dole ba za ta sauke shi ba tare za su mutu kamar yadda ita ma Talatuwar za ta tafi da ita. Malam Mammani a sukwane ya shigo, yana zabgar nasa salatin dan yana jin kuka ya ji ya yi kama da na mutuwa, dan haka yana zuwa ya yi sufa har neman faɗuwa yake, sai ga shi a gaban Talatuwa ya yi zaman ƴan bori, haka ya wangame baki yana kuka yana faɗin "Annabi ya san da zuwanki Talatuwa, Allah sa har a aljanna ke matata ce" Ya faɗa yana kauda kai gefe ya wani face majina ya goge da hannun rigarsa yana cigaba da kuka tamkar wani ƙaramin yaro haka suka kwatsu suna kukan tamkar dai an ce idan suna kukan za ta dawo. Yana cikin kukan nan Gwaggo ta dakata da nata kukan ta sauke hannun nan nata daga baya inda ta danne Nasiru, ta ɗauki wani murfin silbar da aka kawo wa Talatuwar ruwa ta ɗaga ta sauke wa Malam Mammani a fuska dan a daidai inda hancinsa yake ta ƙwala masa zafin da ya ziyarce shi ne ya sanya ya yi ɗif daga kukan da ya dage yana zabgawa. "Kai Mammani rufe ido ba makanta bane, kuma duk girman dutse bai kai ƙaramin goro ba, kuma wallahi bar ganin ka tara ka kiyayi mai nema, in banda dai son a sani gaida uwar miji a kasuwa, ka je har gidan mijina ka rabo ni da makawancina kana ganin na saka hannu zan duba yaro, yaron ya totsa hannuna ya riƙe maƙatau ƙofar da zan janyo hannun ma ta rufe ruf sai lanƙwasa mini yatsu ake, yanzu kuma matarka ta cika (Ta mutu) Ni kuma tun da, da sauran kwanana maimakon ka san yadda za a yi in kuɓuta, sai kawai ka zo kana addu'ar ta zama matarka a aljanna" Ta faɗa cikin muryar kuka. Galala Malam Mammani ya saki baki yana kallon Gwaggo dan shi yadda ya ji zafin dukan murfin silbar ma sai ya rasa bakin magana dan sai a lokacin ma ya lura da cewa hannun Gwaggon yana maƙale a ciki mamaki al'ajabi su ne suka ziyarce shi kafin daga bisani wani bala'in tsoro ya masa dirar mikiya a zuciyarsa, a take ya haɗiye ɗan sauran kukan da yake son ya cigaba da rerawa dan ya fara tunanin ma ya tashi ya gudu. Bai yi magana ba, ɗakin kuwa baka jin komai sai gunjin kukan Kaka, bai yi ƙasa a gwiwa ba ya fara lallaɓawa yana ƙoƙarin tashi, dan shi ya fara tunanin idan ya fita daga ɗakin babu abin da zai ƙara dawowa ya yi. "Taɓ! Tabbas ana marin matacce ne dan mai rai ya ji tsoro, wallahi yau sai dai a yi wacce za a yi ɓera ya zubda garin mage, wallahi babu abin da zan tsaya yi dan yau na ga abin al'ajabi budurwa da ciki gwauro da yaye" Ya faɗa a ransa yana haɗiye wani yawu muduk. Yana daf da tashi Gwaggo ta saka hannunta ɗaya ta danna shi ya koma ya zauna cikin hargagi ta ce "Mammani bari ka ji in faɗa maka wallahi abin ba zai iyu ba auren ɓera da mage, in banda abin ba'a ne an ce da kare mai sunan maza, ta yaya kai da muka taru a nan sabo da kai amma kake neman ka cikawa rigarka iska, ni ka bar ni da hannu lunƙume a jikin matacciyar matarka to ba za ta saɓu ba bindiga a ruwa" Gwaggo Ramma ta faɗa tana aika masa saƙon harara. "Keeee! Ke ɗin ma ki rufewa mutane baki, wallahi ku san yadda za ku yi ku fitar mini da hannuna daga jikin gawar nan, in ba haka ba daga ke har shi sai na mayar da ku ƙananun kiyashi, yadda babu wanda zai samu damar ganinku ma bare har ku bada labarin abin da ya faru" Gwaggo Ramma ta faɗa tana kallon Kaka da ta daddage tana rafka kuka, da Malam Mammani da ya koma ya yi zaman raƙumi sanadin durƙusar da shi da Gwaggon ta yi. Daga Kaka har Malam Mammani suka shiga mummunan tashin hankali jin furucin da Ramma ta yi, domin kuwa sun san sabo da bokancin marigayin ubanta kowa yana tsoron sharrinta. Haƙuri suka shiga bata amma fafur ta ƙi haƙura ta ce sai sun san yadda suka yi suka fito mata da hannu nata, kafin a sanar da kowa mutuwar, hatta matan gidan ma suna jin kukan amma basu san abin da yake faruwa ba. Kakar tashi ta yi daga kusa da Talatuwar ta dawo bayan Gwaggo ta ce "Mammani, tashi ka kama Talatuwar ni in kama Ramma, sai mu ringa fisgarta ko Allah zai sa hannun ya fita... "Sannu sara mai baƙin takashi, ga ki bulu ga ki jaja-jaja, wato ku ke fisgata sai ka ce wata akori kura, son a je ni ba a fitar mini da hannu ba a je hannun ya guntule gaba ɗaya in tashi daga Ramma UNGOZOMA in koma Ramma mai dungulumi" Gwaggo ta katse mata maganar. Malam Mammani kuwa shi gaba ɗaya an dagula masa lissafi jin an ce shi ne zai kama gawar, yana ganin ta yaya zai kama matar da ɗan jinjirin cikinta ya maƙale hannun UNGOZOMA, har da lanƙwasa mata yatsu lamarin da yake ƙara dulmiyar da shi kogin tsoro. "Ka kama ta cikin dibara ku fitar mini da hannuna dan idan dai kuka bari muka yi mutuwar kasko da ita, aka binne mu, to kuwa ku ma ku sani naku kwanakin sun ƙare" Gwaggo Ramma ta faɗa cikin halin ko in kula. "Ko dai in samo bushashshiyar kuɓewa, sai a dama da ruwa a shafa a hannun ko sulɓin zai sa hannun ya fito" Ya faɗa a ransa yana jin ya samo mafita, ba sai ya taɓa gawar ba dan yanzu a halin da ake ciki taɓa gawar shi ne babban tashin hankalinsa. "Bari in samo wani magani zai taimaka sosai" Ya faɗa cikin rawar muryar dan yana tunanin ko ba lallai bane Rammar ta amince. Shiru ta ɗan yi tana tunni da nazari a kan maganar, kafin cikin bada umarni ta ce "Na yarda in dai magani ne, amma ka sani idan ka gudu ka ƙi dawowa, wallahi ni kaɗai na san hukuncin da zan maka" "Wallahi babu inda zan je maganin kawai zan samo" Ya faɗa yana jin daɗi a ransa dan ya hango yadda zai yi ba tare da ya taɓa gawar ba. Buguzum-buguzum ya tashi ya fita, jim kaɗan sai ga shi ya dawo ɗauke da wani kwano, da ya ɗakko kuɓewar da ya jiƙa, yana shigowa ɗakin sai ya tarar da Gwaggo Ramma tana karkarwa, ita kuma Kaka ta raɓe a jikin bango ita ɗin ma karkarwar jikinta yake kamar mazari, a tsorace yake kallon su yana son gane asalin abin da ya firgita su lokaci guda daga fitarsa. Da hannu Kaka ta shiga nuna masa gawar, da rashin fahimta yake kallon gawar dan duk tunaninsa ma ko ba mutuwa ta yi ba, amma abin da ya ƙara dagula masa lissafi ganin tana nan a yadda take tun farko, yanzun ma a haka take, wato tana kwance a reran kanta ya karkata gefe. "Ci, ci, cikin Talatuwa Kaka ta faɗa cikin ciccira maganar sabo da tsabar ruɗun da take ciki. A hankali ya ɗaga idanun nasa ya sauke a kan cikin nata, abin da ya gani ne ya haifar masa da wata iriyar zabura sabo da tsoro, ƙafafunsa suka sage suka fara karkarwa tamkar wanda yake rawa a gaban makaɗi, har hakan ya haifar da faɗuwar kwanon da ya shigo da shi mai ɗauke da kwaɓaɓɓiyar kuɓewa. *GIDAN MAI GARI* "Ni wallahi ban taɓa ganin baƙar jaraba irin wannan ba, haka kawai babu gaira babu dalili ka saka mu a cikin masifar da fitowar ta sai wanda ya gani" Salele ya faɗa cikin raɗa shi ma yana sakin na shi marayan kukan marar sauti. "Aikin banza roƙon a gidan kurma, wannan abin ai sai ido bebiya ta auri makaɗi" Mai Gari ya faɗa hawayen tausayin kansa suna gangaro masa, da sauri ya kai hannunsa wajen kansa jin inda ya ɗora kansa yana masa zafi domin kuwa a kan ƙurunƙusan tsakuwar ɗakin ya ɗora kan. *LAILA* Tun da suka fita suka bar ta a ɗakin, ta yi kwanciyarta a kan gadon ƙarfen Gwaggo wanda dakyar ya ɗauke ta, duk da haka sai ƙiƙar-ƙiƙar yake tamkar zai ruguje. Kwanciyarta ke da wuya bacci ya ɗan fara ɗaukanta, sai kawai ta ji alamun tusa tana neman hanyar fitowa, a kiɗime ta tashi zaune ta shiga ƙwalawa Taju kira dan ya zo ko da a kansa ne ko kuma wani mai rabon ta saki tusar, sabo da ta san tabbas idan ta saki tusar ba tare da ta zauna akan kowa ba to akwai matsala, domin kuwa tsagar mazaunan nata ce take ƙaruwa, sai wurin ya tsage amma matuƙar ta zauna a kan wani to babu abin da zai faru da ita, hakan ne ma ya sanya ba ta yarda ta yi tusa sai ta zauna a kan mutum, dan wani lokacin har kuɗi take biyan mutane ta zauna a kan su ta yi rusar. Tun da ta fara kiransa ta ji bai amsa ba sai hankalin ta ya tashi, jin tusar tana neman fitowa sai ta fara ƙoƙarin sama wa kanta mafita ta hanyar tasowa ta buɗe ƙofar ta fito domin zuwa ɗakin da su Tajun suke ko ta samu ta kai farmakin yin tusar tata a kan mai rabo, dan duk wanda ta fara samu to kakarta ta yanke saƙa, haka ta fito riƙe da fitila. Su Mai Gari kuwa tun da suka ji motsin ƙofa suka ƙara shiga halin ƙaƙanika yi. "Shikenan kuma mu yau sai yadda hali ya yi karuwa ta ga ɗan sanda, nin banda tashin hankali faɗa da mai gari ranar sallah, ya za a yi a ce sai an zauna a kan mutum za a saki tusa sabo da Allah kamar wanda aka samu kujera" Cewar Mai Gari a ransa yana jin kamar ya yi tsuntsuwa ya gudu dan kar Laila ta ritsa da shi. Jin ta turo ƙofar ɗakin sai kowa ya yi lif tamkar masu bacci har da masu sakin munshari a kai - a kai. a firgice ta shigo tana neman ɗauki sanadin jin tusar tana dab da fitowa. Tana shigowa sai ta haska fitila ai kuwa ta gan su kwance sun yi murhu da kawunansu. "Shikenan tusa ta za ta fito cikin salama, tun da ga shi a kawunan mutane har uku zan sake ta" Ta faɗa a ranta tana nufar su cikin sassarfa, tana zuwa ta daddage ta ɗora mazaunanta a kawunansu inda suka yi murhun tana ɗorawa kusa tusar kamar jira take a fito da wani irin ƙara da ya bada sautin booottttt. Fitar sautin tusar ne ya sanya kunnuwansu yin dimmm tare da ɗaukewar jin su na sakkanni. Sai kuma lokaci guda wani uban wari mai kamar mushen akuya ya mamaye gaba ɗaya ɗakin. Laila kuwa sake ɗan karkata mazaunan nata ta sake yi domin wata tusar ta samu damar fitowa. "Kin kashe mu" Mai Gari ya faɗa jin wari da nauyin danne su ɗin da ta yi yana bazaranar sumar da shi. "Wayyo an saka hancina a tekun maliyar kashi" Salele ya faɗa yana ta ƙoƙari ya samu inda hancinsa zai shaƙo masa wata iskar ba wacce yake shaƙa ba mai wari da ɗoyin tsiya... Maman Afrah Wtsapp 09013181851 *META FORCE ARZIƘI DAGA ALLAH* ƳAR UWA SHIN BAKI DA LABARIN META FORCE? DA IRIN ƊINBIM ARZIƘIN DA AKE KWASHEWA A CIKINSA, YA AKA YI BAKI YI REGISTER BA? KO BAKI DA BUƘATAR KUƊAƊEN DA ZA KI YI HIDIMAR YAU DA KULLUM? TO KI ZO NI MAMAN AFRAH NA ZO MIKI DA HANYAR SAMUN KUƊI TA WAYAR HANNUNKI KUƊIN YIN REGISTER KAWAI ZA KI TANADA 9K DUBU TARA DOMIN ANA YIN REGISTER DA DALA 5 NE SAI DAI ALLAH KAƊAI YA SAN IRIN RIBAR DA ZA KI SAMU DA KUMA ALKAIRAN DA YAKE CIKIN KASUWANCIN. IDAN KINA SO SHIGA KUMA DA GASKE KIKE KI MINI MAGANA A WANNAN NUMBER 09013181851 IDAN BA YI ZA KI YI BA KAR KI MINI MAGANA DAN BANA SON ƁATA LOKACI! [8/19, 17:57] Mom mashkur & Afrah: UNGOZOMA (Mai karɓar haihuwa) NA MAMAN AFRAH FCW GARGAƊI⚠️ Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ta kowace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowace kafa ba sai da izinina a kiyaye. Ina mata ƴan ƙwalisa, babbar mace alkyabbar mata, macen mai gyara ita wacce ta isa da miji su o'o sai dai su ga ƙeyar mijinta idan ya wuce amma basu ishe shi kallo ba domin babu abin da za su nuna mata. Gyaran gashi babbar martaba ce da take ɗaga darajar mace, musamman kayan gyaran gashin MAMAN ZEE da ya yi fice a ko ina ake labarinsa. Gani ya kori ji sai an gwada akan san na ƙwarai siyan na gari mayar da kuɗi gida💃💃💃💃💃💃💃💃 Hadaddu Kuma ingantattun kayan gyaran gashin mamanzee(chebe hair set) Wadanda suke dawowa da martabar gashin Kai komai lalacewarsa biiznillahi Rabbi Ga kyau ga inganci ga saukin kudi muddin kika fara amfani da kayammu sekindawo Mana da kyakkyawan labari Kanki zeyi kyau ya rika sheki yayi tsayi yayi laushi duk matsalar da ke cikin kanki zata kau in sha Allah Munada set complete Kuma Muna Bada pieces Haka Kuma Muna Bada Sari Muna turawa akowanne gari kike Kuma Ako wacce kasa kike Phone number *08079130166* Page 1️⃣5️⃣➡️1️⃣6️⃣ *MALAM MAMMANI* Ƙurawa inda yake kallon ido ya yi, ganin dai tabbas ba gizo idanun nasa suke masa ba sai ya ƙara shiga mummunan tashin hankali, lokaci guda ya ji maƙoshinsa ya bushe. "Jama'a kuna ganin abin da nake gani kuwa? Yadda nake ganin cikin Talatuwa yana rausaya ubangiji ya nuna mini annabi haka" Gwaggo Ramma ta faɗa cikin sumbatu. "Lahaula wala quwwata illah billahi aliyal azim, rabbi lima anzalta ilayya min kairin faƙiir" Malam Mammani ya faɗa yana jin jikinsa har wani zafi yake ɗauka kamar wanda zazzafi ya rufe. "Wallahi ƙur'ani muna gani Ramma ba ke kaɗai kike gani ba" Kakar Talatuwa da abin ya so zautarwa ta faɗa a tsorace. Suna cikin hakan sai kawai suka ga bulll, jaririn ya bullukuto kan nasa ta tsakiyar cikin Talatuwa sai dai iya kansa ne kaɗai ya fito, gabaɗaya sun ma manta da maganar mutuwar Talatua bare su ce ita ce take motsi, tun da dai sun san ta mutu, musamman Gwaggo Ramma da hannunta yaƙe ƙunshe a jikin Talatuwa. Tun da ya fito da kan yake ta rausaya kan alamar rawa, gaba ɗaya kasaƙe suka yi dan sun yi mutuwar tsaye suna ganin ikon Allah, musamman Gwaggo Ramma da ta ga saitin ta yake kallo, kafin su gama tantancewa sai gani suka yi ya yi tsalle ya fito daga cikin Shamsiyya yana rarraba ido. Hannunsa ɗaya riƙe da cibiyarsa da uwa wacce take faɗowa idan an haifi jarirai. Babu zato ba tsammani ya buɗe baki ya tsanyara kuka irin na jarirai. "Gwara dai in yi kukan da kowane jariri yake idan ya diro duniya" Ya faɗa yana ƙara rausaya kan nasa tamkar wani ƙadangare. Kukan sa ya yi shi ya sanya matan gidan da suka jiyo kukan suka tabbatar Talatuwa ta haihu. A daidai gaban Malam Mammani ya dira, ƙafafunsa suka sauka a kan kuɓewar da ta zube, jin santsin ledar tsakar ɗakin zai kayar da shi sai ya yi saurin miƙa hannunsa wanda babu komai ya kamo rigar Malam Mammani, Malam Mammani kuwa mutuwar tsaye ya yi, a take ya ji numfashinsa ya tsaya cak jikinsa ya cigaba da rawar tamkar dai wanda aka saka a firiza. "Baba wallahi na kusa shan ƙasa, Allah ya sa kana kusa Babana da tuni santsin kuɓewar nan ya daɗe da tiƙa jaririn da ya dira duniya yanzu-yanzu da ƙasa" Cewar jaririn cikin muryar yara ƙanana masu koyan magana. Malam kuwa idanunsa ya sauke ƙasa suka sauka a kan jaririn da ya kira shi da suna Babansa. Gwaggo kuwa tun da ta ga jaririn ya nufi wajen Babansa sai ta bada himma wajen karanta addu'a a hankali tana tofawa a hannunta da yake maƙale, duk da tana rattabo addu'o'in ne ba tare da ta san ita kanta addu'ar me take karantawa ba. Dan tana ganin yau mai dogon kwana kaɗai ne zai fita daga ɗakin dan ita yanzu ta daina jin nauyin goyon Nasiru da take ɗauke da shi dan gaba ɗaya tashin hankalin da take ciki ya danne nauyin goyon bayanta. Cikin ikon Allah sai ta ga ƙofar ta buɗe, hannun nata har karkarwa yake wurin fito da shi daga jikin Shamsiyya, tana fitar da hannun kuwa ƙofar ta koma ya rufe. A ranta tana ƙiyasta yadda za ta fice ta gudu daga ɗakin ta bar ma gidan baki ɗaya. Baram, ƙaran rufe ƙofa ya yi dirar mikiya a kunnuwan Gwaggo. Da sauri ta yi wani juyin tamkar yadda ake juya muciya idan ana tuƙin tuwo, ai kuwa ta hangi jaririn nan a jikin ƙofa ya rufe ta ruf ya jingina bayansa a jikin ƙofar yana kallon ɗaya baya ɗaya. "Ni Ramma yau wace rana ma muke, da wannan sankata-sankatan ƙaddarori suke faruwa a ce jariri ya fasa cikin matacciya ya fito da kansa yana tafiya har da magana abu bai tsaya a nan ba har da su rufe ƙofa" Cewar Gwaggo a ranta tana kallon inda Kakar Talatuwa take a raɓe tamkar ka ce kulle ta ce cass iIdanuna nata ta juya ta kalli Malam Mammani ta wutsiyar ido motsin bakinsa kawai take iya gani, dan bakinnnasa sai lamisawa yake kamar bakin tsohon da babu haƙora a ciki sai kuma yatsunsa da yake ta lazimi da su. "To uban ɗan ma kenan bare kuma ni UNGOZOMA" Ta sake faɗa a ranta tana jin ina ma ba ta taho karɓar haihuwar ba, tana ganin ta baro Laila a gida tana ganin su Mai Gari suna can ana karɓar gashin aya a tafin hannu ashe dai a nan ma wata uƙubar za ta karɓa Jariri kuwa takowa ya fara yi har lokacin uwa da cibiyarsa suna riƙe a hannunsa, yana zuwa saitin Malam Mammani kawai sai gani aka yi ya tashi kamar mai tafiya a saman iska bai tsaya a ko ina ba sai a tsakiyar kan Malam Mammani. Malam Mammani jin saukar ƙafafun jaririn a kansa sai kawai ya ji tamkar an ɗora masa iccen wuta, a hankali ya shiga ɗaga idanunsa sama, ai kuwa sai ya hangi jaririn yana tsaye a kan nasa. Kafin ya gama wannan mamaki sai gani ya yi an zuro cibiyar zarere tana reto a saitin fuskarsa ta sauka har wajen ƙirjinsa kallon cibiyar kawai yake tamkar ya ga ajalinsa sabo da yadda yake jin bugun ƙirjinsa. "Ayyuhan nassss, ku saurara, zan yi muku kuɗubar juma'a duk da yau ta kasance ba juma'a ba" Jaririn ya faɗa cikin muryar jarirai amma kuma yana mata ƙalƙala da maganar uztazai. Wani fitsari ne kawai ya ƙwacewa Malam Mammani, dan shi dai yau ya ga annoba shiga wutar kara. Kakar kuwa da ta ga jaririn ya ƙwalalo mata idanu lokacin da yake magana sai kawai ta sunkuyar da kai ƙasa. "Ya Kakar Ummata, shin baki ga na hau minbari ina muku kuɗuba ba? Amma kika sunkuyar da kai" Da sauri ta fara yaƙi da bakinta har dai ta samu nasarar finciko maganar. "Na'am,na'am na'am ya jinjirin jikata" Cewar Kaka cikin muryar ustanzanci dan ta ga abin yana neman fin mai rai sai dai ko matacce. "Ungo..." "Na'am ya shaik ai tuni mun ji mun bi, kuma mun yi imani da Allah da ranar lahira" Cewar Gwaggo Ramma cikin sauri tun bai gama kiran sunan nata ba. Haka dai ya cigaba da surutansa wani ma ba sa gane abin da yake faɗa. Ƙafarsa ya ziro fuskar Malam, sai da ya kai ta daidai hancin Malam ɗin sai ya tura babban yatsan ƙafarsa a ƙofar hancin Malam ɗin, Malam kuwa yana nn kamar an dasa shi ya kasa cewa uffan sai addu'a da yake a zuciyarsa a kan Allah ya fitar da su daga cikin wannan bala'i. Sai da ya gaji dan kansa sannan ya fito da ƙafar. Jim kaɗan sai kawai ya taso luuuu daga saman kan Malam Mammani bai yi masauki a ko ina ba sai a bayan Gwaggo Ramma wato ya sauka a kan bayan Nasiru da yake bayanta. "Shikenan kuma yau ba zama an ɗaurawa karya zani, an ringa hawa da sauka babu tsayawa sai inda mai ya ƙare shiga motar mahaukaci" Cewar Gwaggo a ranta a fili kuma sai ta ce. "Rabbana atina fid duniya hasana wa fil akirati hasana a ƙina azabar naar" "Sannu Ramma, ina askar yankan cibin naki ki ɗakko ki yanke mini cibiya" Ya faɗa har lokacin yana bayanta a kan Nasiru. "Yo ni ai jariran da aka haifa nake yankewa cibiya amma kai kuwa da kai ka haifi kan ka, ina ni ina taɓa maka cibiya haka kawai in shiga tara" Ta faɗa a ranta. "Ko in ɗakko miki askar da zaren lilon da kike ɗaure cibiyar?" Ya ƙara katse mata tunani, Malam kuwa da Kaka har lokacin suna ta ambaton Allah ko dakatawa ba sa yi. "Ni yau ai son kaje ka saka ni a kogin da zan kasa fitowa wallahi, domin wannan ai wayon a ci ne an kori kare daga bakin ɗinya, wannan ɗan na bayana da ka danne shi girman uwarsa ya fi gaban wasa, dan za ta iya yin ƙuli-ƙulin kubura da ni ba tare da ta saka fulawa ba, ɗan amana ne dan idan wani abu ya same shi na san na kaɗe daga ni har su Mai Gari da basu san hawa ba su san sauka ba. " Ta faɗa a zuciyarta. "Ba za ki yanke min cibiyar ba?" "Za a yanke maka" "To maza un go fara aikin ki" Ya faɗa yana miƙo mata cibiyar saitin fuskarta kafin ta samu zarafin magana ya yi tsalle ya diro gabanta. "Wannan uwar a binne ta"Ya faɗa yana miƙa mata uwar mahaifar, da hannu biyu ta karɓa sai kuma ya saki cibiyar take binsa zaroro. "Ki ajiye uwar mahaifar duk ku dawo nan za mu yi wasa" Ya faɗa lokacin da ya koma gaban Malam Mammani da yake tsaye kamar gunki. Kallon kallo aka fara amma ganin ya kafe su da ido sai kowa simi-simi ya taso ya ƙaraso gabansa ga tsoro ga kwanan yunwa. Su duka ukun ya saka suka hau layi kamar na sahun sallah, Gwaggo da take goye da Nasiru sai lokacin ta ƙara jin bayanta yana ƙage sosai. Suna tsaye suna kallon ikon Allah. Amma shi Malam Mammani abu biyu ne ya haɗe masa goma da ashirin ga tsoron gawar da take kwance a tsakar ɗakin ga kuma tsoron jaririn da yake gabansu yana sabgarsa tamkar wani mai shekara hamsin. Kaka kuwa idanunta ta sauke a kan gawar Shamsiyya ganin cikin nata inda jaririn ya fito ya rufe kamar ma ba ta wurin ya fito ba, hakan ya sa ta ƙara shan jinin jikinta dan tana ganin wannan abu mai kamar almara tun da take bata taɓa ganin ɗa ya fito ta ciki ba sai dai a ce an yi tiyata an fito da shi amma kuma yau ga shi abin ya faru a kan idanunta ita yanzu gaba ɗaya ma tsoro ne ya lulluɓeta har gawar ma yanzu tsoronta ya cika mata zuciya. Bare kuma Gwaggo da take jin kamar bangon ɗakin ya tsage ta runtuma a guje ko waiwaye babu. Ƙafa ɗaya ya ɗage ɗayar kuma ya saka a cikin kuɓewar da take malale a tsakar ɗakin sululuuuuu ya tafi da ƙafa ɗaya. Cikin ƙwarewa yake ta zagaya tsakar ɗakin yana ta dariya cibiyarsa tana binsa su kuma gaba ɗaya sai lamarin ya ƙara tsorata su, sai da ya yi zagayen sau goma amma ko faɗuwa bai yi ba duk da kuɓewar da tsantsin ledar ɗakin. "Za ku fara zagayawa kamar yadda na yi amma ku duka ukun a tare za ku yi" "Haba ɗan albarka kai kuwa mutumin nan baka ganin gawa a ɗakin amma sai mu ɓige da zagaya ɗaki" Malam Mammani ya faɗa cikin muryar kuka dan shi abin ya ishe shi domin abin ya yi yawa wai shege da hauka, yana fatan Allah ya kawo wanda zai kawo musu ɗauki. "Ni ba mutumi bane ɗan jinjiri ne, kuma da ka ke maganar gawa ba gawar uwata bace, ai muna gama wasan sai ku je ku binne ta" Ya faɗa fuska a ɗaure. Babu wanda ya ƙara cewa ƙala haka suka fara ƙoƙari cika umarninsa. Kafin su fara sai gani suka yi ya yi tsalle ya maƙale cibiyarsa a jikin wani ƙarfe a saman ɗakin sai ya zamana yana rataye yana reto a jikin cibiyar tamkar wanda yake lilo. Malam Mammani da jikinsa yake karkarwa haka ya ɗaga ƙafa ya shiga cikin kuɓewar duk da dama jaririn ya gama haɗa tsakar ɗakin da kuɓewar taku ɗaya Malam Mammani ya yi a cikin kuɓewa bai ankara ba sai ji ya yi ya tafi luuuuuu lo tsayawa babu tun daga inda yake sai da ya je ƙarshen ɗakin ya je a zaune daɓas faɗuwar da ya yi sai ya ji tamkar wurga shi aka yi. Gwaggo da Kaka suna ganin haka sai suka shiga tashin hankalin da ya fi na farko musamman Gwaggo Ramma da take ɗauke da goyo a bayanta. "To ku ma ku tafi a tare" Muryarsa ta katse su har lokacin yana maƙale a saman ɗakin yana ta reto. Babu musu haka su Kaka suka ɗora ƙafafu a kan kuɓewar su ma, suuuu kake ji sun tafi da yake ɗakin yana da girma, Gwaggo ce a gaba Kaka tana baya. "Kar wacce ta kuskura ta yarda ta faɗi kuke ta zagaye ɗakin" Ai gaba ɗaya sai suka daddage dan ganin basu faɗin ba sai suke gewaye ɗakin tamkar masu yawo da takalmin taya. "Kai ma ka tashi ka bi sahu, ka jaɓe a waje ɗaya daga farawa" Malam Mammani ya ji muryar jaririn ta katse shi. "Bismil ƙadari maganin masifa" Ya faɗa a ransa yana tashi dakyar jin ƙugunsa kamar ma ba a jikinsa yake ba. Sahun su Kaka ya ci kowa sai baza hannuwa yake irin kamar za su faɗin nan, Kaka jin za ta faɗi aikuwa ta kamo Nasiru da yake bayan Gwaggo, haka ya yi daidai da miƙa hannun Malam ɗin ya kamo zanin Kaka, Kaka jin an damƙo zaninta a take ta saki Nasiru ta damƙe zaninta da hannu biyu tana sakin salati dan ta ɗauka jaririn ne ya ja zanin zai mata tsirara a cikin mutane, haka da ta yi shi ne ya assa sa Gwaggo ta yi sufa, Kaka ta bi bayanta sai Malam ma ya bi bayan Kakar Gwaggo a saitin gawar ta faɗi sai ya zamana kanta a kan cikin gawa, kaka kuma ƙirjinta ne ya sauka a kan ƙafafun gawar, Malam kuma fuskarsa ta sauka a kan fuskar gawa. "Kowa kar ya motsa daga yadda yake" Muryar jaririn ta katse musu hanzari. "Mu karanta lahaula ƙafa bakwai Allah sa kar gawar nan ta manne da jikinmu a mana sitira a binne mu tare" Malam ya faɗa cikin muryar kuka da tsantsar tashin hankali. "Wayyo Allah, na kasa banbance alif da ambaki, gga goyon ɗan ruwa ga ni a kan gawa ga jariri yana tijara Allah ka kaow maa ɗauki ka kawo mai ceton mu" Gwaggo ta faɗa ranta tana jin tamkar ta yi filfilwa ta bar jikin gawar. "Haba Malam Mammani, in ban da abinka ina muka ga nutsuwar da za mu iya karanta lahaula, lahaular ma ƙafa ɗai-ɗai har ƙafa bakwai? Ina laifin ma ka ce ƙafa ɗaya idan abin ya yi tsamari mu karanta ƙafa uku, ni wallahi ba zan ma iya lissafa wa ba a halin da nake ciki yanzu na rayuwa ko mutuwa" Kaka ta faɗa tana rushewa da wani marayan kuka. "To Kaka ai sai mu karanta yadda ya sauwaƙa tun d... Maganarsa ce ta katse jin saukar jaririn a tsakiyar kansa, tsalle jaririn ya shiga yi a kan Malam idan ya yi tsallan sai fuskar Malam ta manne da fuskar gawar tsananin tsoron da yake ciki na ganin fuskar gawa a jikin fuskarsa muraran sai ya saki kuka amma sabo da tijara jaririn nan bai bari ba sai da ya tabbatar ya gama sanya Malam a ruɗani sannan ya yi tsalle ya sauka a kan Gwaggo idan ya yi tsalle sai goshin Gwaggo ya manne da ciki gawar, goshin nata kuma a saitin inda jariri ya fasa ya fito, Gwaggo bakinta ne kawai yake motsi amma ita kanta ba ta san abin da take cewa ba sai ruwan hawaye kamar wanda aka ce kar ta daina zubo da su. Sai da ya tabbatar sabo da tsabar tsoron Gwaggo ko yatsanta ba za ta iya ɗagawa ba sabo da yadda ta tsure yana gamawa ya yi tsalle ya sauka a kan Kaka da ta gama tsurewa ma, idan ya yi tsalle a bayanta sai ƙirjinta ya manne da ƙafafun gawar, fat-fat-fat kawai kake ji, sabo da tsabar yadda ƙirjinta yake bugawa tamkar zuciyarta za ta fito dan a duniya duk abin da take tsoro to ya bi bayan gawa. Yana gamawa ya sauka ya je saitin hannun gawar ya maƙala cibiyarsa a hannun nata sai ya nannaɗe ta. "Mu je zuwa gawar mama" Suka tsinkayi muryarsa, Gwaggo da sauri ta miƙa hannu ta damƙo aska da zarenta, na aikin UNGOZOMANCI basu ankara ba sai suka ji ana yin sama da su ma'ana gawar ta tashi da su, kowa baki yana karkarwa yake kiran sunayen Allah, haka suka shiga shawagi a ɗakin "Allahumma salli ala muhammadin" Malam ya daddage ƙarfinsa yana faɗa tsabar ruɗewa. Kowa ya dage da addu'a babu sassutawa, suna cikin yin addu'a sai kawai suka ji gawar ta sauka ƙasa, ɗifff suka ji a kiɗime kowa yake kallonsa yashe a gefe guda kamar an jefar da shi. Kallon ɗakin suke amma babu jariri babu alamarsa, ga Talatuwa nan kwance da cikinta a jikinta Gwaggo da sauri ta tashi tsaye a kiɗime duk da santsi yana ɗaukanta amma babu abin da ta tsaya yi ta nufi ƙofa ta buɗe ta fice ko takalminta ba ta tsaya ɗauka ba ta nufi hanya ta fice daga gidan, tinƙan-tinƙan ta kama hanyar gida ko tsoro babu sabo da tana ganin halin da ta baro na tsoron gawa ya take kowane tsoro a ranta. Haka ta zo ƙofar gidan nasu tana hakin goyon Nasiru da yake bacci har lokacin kamar gawa, tana zuwa ta shigo gidan a kiɗime so take kawai ta ganta ta shiga ɗakinta ta rufe. Tana ƙarasowa barandar wani ƙara ya mata sallama a kunnuwanta wanda ba ƙaran komai bane sai na tusar Laila da ta ƙara saki a kan su Mai Gari. MAMAN AFRAH 09013181851 *META FORCE ARZIƘI DAGA ALLAH* ƳAR UWA SHIN BAKI DA LABARIN META FORCE? DA IRIN ƊINBIM ARZIƘIN DA AKE KWASHEWA A CIKINSA, YA AKA YI BAKI YI REGISTER BA? KO BAKI DA BUƘATAR KUƊAƊEN DA ZA KI YI HIDIMAR YAU DA KULLUM? TO KI ZO NI MAMAN AFRAH NA ZO MIKI DA HANYAR SAMUN KUƊI TA WAYAR HANNUNKI KUƊIN YIN REGISTER KAWAI ZA KI TANADA 9K DUBU TARA DOMIN ANA YIN REGISTER DA DALA 5 NE SAI DAI ALLAH KAƊAI YA SAN IRIN RIBAR DA ZA KI SAMU DA KUMA ALKAIRAN DA YAKE CIKIN KASUWANCIN. IDAN KINA SO SHIGA KUMA DA GASKE KIKE KI MINI MAGANA A WANNAN NUMBER 09013181851 IDAN BA YI ZA KI YI BA KAR KI MINI MAGANA DAN BANA SON ƁATA LOKACI! [8/19, 17:57] Mom mashkur & Afrah: UNGOZOMA (Mai karɓar haihuwa) NA MAMAN AFRAH F.C.W GARGAƊI⚠️ Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ta kowace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowace kafa ba sai da izinina a kiyaye. Hadaddu Kuma ingantattun kayan gyaran gashin mamanzee(chebe hair set) Wadanda suke dawowa da martabar gashin Kai komai lalacewarsa biiznillahi Rabbi Ga kyau ga inganci ga saukin kudi muddin kika fara amfani da kayammu sekindawo Muna da kyakkyawan labari Kanki zeyi kyau yarika sheki yayi tsayi yayi laushi duk matsalar da ke cikin kanki zata kau in sha Allah Munada set complete Kuma Muna Bada pieces Haka Kuma Muna Bada Sari Muna turawa akowanne gari kike Kuma Ako wacce kasa kike Phone number 08079130166 Page 1️⃣7️⃣➡️1️⃣8️⃣ "Ikon Allah na zaune ya faɗi, ƙaran mene ne wannan kamar motar tan-tan ta wuce?" Gwaggo Ramma ta faɗa a zuciyarta gabanta yana matsanancin bugu tamkar ana bugawa da guduma. Cikin sanɗa ta fara lallaɓawa ta tura ƙofar ɗakin nata, ta shige tana shiga amma ganin kayan Laila a ɗakin ta hasken farin watan da ya haska ɗakin sai gabanta ya faɗi, cikin kiɗima ta juyo ta fito daga ɗakin dan ganin kayan ya ruɗa ta, domin hakan yana nuna mata kenan ɗakin ya zama mazaunin Laila kuma ita alal haƙiƙa ko ana ha maza ha mata babu abin da zai sa su haɗa ɗaki da wannan matar mai kamar dunƙulalliyar giwa. Duk da tunaninta bai bata ta tuna inda sauran mutanen gidan suke bare ma mai gayya mai aiki Laila, amma a haka ta yanke hukuncin shiga ɗakin Salele dan tana ganin can ɗin tamkar hanyar tsira ne, sai ma ta shiga tunanin cewa ƙaran da ta ji wataƙila ma kawai gizo ne kunnuwanta suke mata. Tana zuwa ƙofar ɗakin baram ta bankama kofar ta shige, hasken fitilar Laila da ke yashe a tsakar ɗakin shi ne ya sanya ta hangi Laila a zaune a kan wani abu wanda tunaninta bai kawo cewa mai gidanta Mai Gari ne da jikokinta ba, dan ita ganin Lailar ya sanya cikin inda-inda ta ce "Allahu akbar kabiran, shi ya sa aka ce tunani baiwa ne nutsuwa da hankali kuma aikin ƙwaƙwalwa ne, rashin sani ne wanda ya fi dare duhu, aradun Allah ranki ya daɗe ba nan na yi niyyar shigowa ba hasali ma ban san kina ɗakin nan ba ki mini afuwa ki yafe ni dan Allah da soyayyar ma'aikinsa kar ki bari allura ta tono garma, na san iya gani iya ƙalewa" Cewar Gwaggo tana ƙoƙarin juyawa za ta bar ɗakin dan tsabar ruɗewa ma bata lura da warin da ɗakin ya ɗumame ba ita kwanciyar hankalinta ɗaya ta bar ɗakin kar ta je Laila ta mata hukunci. Laila kuwa lokacin da Gwaggo take bayanin idanunta a rufe suke tana sauke lumfashi da sauri da sauri tamkar mai naƙudar da ta haihu yanzu, sabo da fitar tusar shi ne samun lafiyar ta da haka ba ta ma san abin da Gwagho take faɗa ba. "Ramma kin ganni manne da mazaunan ranta ya daɗe, tun ɗazu take sakin iska kamar tayar motar lodin shanu, in ban da ma duk nisan tashin tsuntsu sai sama ta ga bayansa ta yaya za a yi matar nan ta danne ni, take sakin iska a kaina ina Mai Gari, yau na tabbatar duk girman dutse bai kai ƙaramin goro amfani ba, amma dai yau na ga fallasa auren bashi domin kuwa wayon a ci ne ya sa aka kori kare daga bakin ɗinya" Cewar Mai Gari a zuciyarsa yana danne hawayen da ke ƙoƙarin kwaranyo masa dan shi haƙiƙa ya san alhakin mutane ne da suke ɗauka, ya sa Allah ya kawo matar nan take azabtar da su. "Gwaggo kin gammu nan fa daga Malam har ni da kuma Taju muna karɓar gashin ƙuma, lallai ba a yi wa uwar kwarto gorin ɗa, ko ba jima ko ba daɗe sai ya dire mata nashi" Salele ma ya faɗa a ransa yana jin nauyin Laila tamkar an ɗora musu duron ruwa. Gwaggo kuwa ko waiwaye ba ta yi ba, ta juya ta nufi bakin ƙofa za ya fice daga ɗakin, har zaninta yana kuncewa tana kamowa ta riƙe da hannu ɗaya dan ɗaya hannun kayan aikin INGOZOMANCIN ta ne. "Ina za ki je kuma" Ta tsinkayi muryar Laila a kunhuwanta tana dab da fita daga ɗakin" Wani uban birki Gwaggo ta ja tamkar motar da ta kusa faɗawa kwalbati. Laila kuwa lokacin da ta daddage ta tashi tsaye domin kuwa ta gama yin abin da ya kawo ta, tashin ta ke da wuya ta hangi Gwaggo tana shirin fita daga ɗakin, dan ita har ga Allah ba ta san Gwaggo ta shigo ba ma. "Dama yaron albarka na kawo miki, wannan yaro mai ɗan karen kirki ko nauyi bashi da shi shafalfal tamkar na goyi leda, ga shi tun da muka je har na karɓi haihuwar nan ko kuka bai yi ba yana ta baccinsa" Gwaggo ta samu kanta da faɗar hakan dan maganar da Laila ta yi ya nuna mata ba ta ma ji abin da ta faɗa ɗazu ba. "Zan sakko" Cewar Nasir da ya tashi daga bacci yanzu. "Ka ga ɗan halak ya ƙi ambato, ashe ma kana kan hanyar tashi daga bacci ni duk tunanina ma baka tashi ba" Gwaggo ta faɗa, kai da ka ganta ka san babu nutsuwa a tare da ita, dan dama har yanzu bata gama dawowa hayyacinta ba daga abin da jaririn gidan Malam Mammani ya musu ba yanzu kuma ta dawo ta tarar da wani sabon salo wai kiran sallah da usur, Dariyar yaƙe ta saki dan ita kwata-kwata ta ƙi jinin haɗa hanya da Laila ko da kuwa ta magana ce, "Mu je ɗakina ki sauke shi" Tun kan Laila ta rufe bakinta Gwaggo ta juya cikin sauri ta fita duk da bata san ma ina ne ɗakin na Laila ba amma dai tun da ta san iya ɗakuna biyu ne a gidan to kuwa kenan ɗakin ita Gwaggon shi ne a matsayin ɗakin da Laila ta ɗauka a matsayin nata. "To ni ƴasu yanzu a ina zan ke kwana ni Ramma, ba dai nufin matar nan ba a ɗaki ɗaya za mu zauna ni da ita tun da mu biyu ne mata ni da ita, haka kawai in je in ke shiga uku da abubuwan da za ta ke mini ko kuwa dai manufarta mu kwatsu a ɗaki laya da Salele da Mai Gari da Taju sai ka ce a gidan arna" Gwaggo ta jefawa kanta tambayar a zuciyarta, sai dai ba ta buƙatar amsa yanzu kuma abin da take so bai wuce ta sauke yaron daga bayanta ba. "Ki kai wa mijinki da jikokin ki taimakon gaggawa" Cewar Laika cikin halin ko in kula tana zaunawa a bakin gadon Gwaggo wanda ya bada saurin " ƙiƙar". "To,to,to" Gwaggo ta faɗa dan son ganin an zauna lafiya, amma ba ta fahimci komai ba a maganar sai dai ta shiga ruɗani jin ta ce a kai musu taimakon gaggawa zuciyarta ba ta barta da tunanin abin da ya samu su Mai Gari da su Salelen ba. Tana fitowa daga ɗakin ta sunkuya a waje tana danna bayanta da hannunta jin wata irin gajiya ta riƙe mata gadon baya, ba komai bane kuwa ya kawo hakan ba sai goyon Nasiru. Tana cikin hakan sai ta fara jiyo ana tari, ana kuma sakin wani nishi daga ɗakin Salele lamarin da ya ƙara jefa kwanyarta a kogin tunanin dan ita dai ba ta ga kowa a ɗakin ba hasali ma ta ɗauka ko su Mai Gari bayan ɗakuna Lailar ta mayar da su. Da ɗan sarsarfa ta nufi ɗakin tana shiga lokacin Salele ya miƙa hannu dakyar ya kunna fitila amma har lokacin babu wanda ya yi wani ƙwaƙƙwaran motsi, sun yi lifet a tsakar ɗakin. Salati Gwaggo ta shiga rattabowa sabo da tunaninta sai ya bata cewar Laila fyaɗe ta yi wa maza guda uku, wato ta tirsasa su suka yi tarayya da ita hakan ya sanya ta ji kishin Mai Gari ya turnuƙe mata zuciya dan ita akwai kishi hakan ne ma ya sanya ba ta son Mai Gari ko da wasa ya raɓi wata mace, amma sai gashi yau a aikin banza a sadaka wata ta zo ta yi mu'amala da mijinta, a gefe guda kuma tana tausayin Salele amma ko kaɗan ba ta ji tausayin Taju ba dan tana ganin shi ya jaza musu halin da suke ciki, domin shi ya kawo musu Laila gida kuma dama ai duk tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa kan duka. "La'ilaha illallahu, muhammadur rasulullahi S.A.W, ni Ramma yau na ga ɗan jijjiɓin hau zalla, yanzu shirmemiyar matar nan ta haike muku ku duka uku rigis sai ka ce ta samu wasu agwagi, fisabilillahi ina laifin ma ta samu ɗan maraƙe (Namijin saniya) Ko dai ta samu (Doki) Ai su ne daidai da ita amma ba mutane ba, yo ina dalili ina ɗan mafari wane ɗan adam ne zai iya da wannan mata, amma dan wulaƙanci gaida sirika da mazaunai shi ne ta zo har da Mai Gari ta haikewa gashi na sai nishi yake kamar an lodowa jaki kaya, to ƙur'anin Allah sai in ja carbi mai dubu in karanta mata addu'ar da za ta saka matantakar ta(HQ) Ta manne tamkar an saka ruwan dalma an rufe tillar kwanon silba, ko wurin ya koma kamar an saka sufagilu an nane kai ko ma wurin ya ɓace ɓat ta neme shi ta rasa dan gani za ta yi babu ƙofar babu dalilinta, in ga nan gaba da wane wurin za ta yi wa wasu fyaɗe" Gwaggo ta faɗa a zuciyarta tana jin kamar ta koma ta shaƙe Laila a kan wannan tozarci da ta yi ko ma ta mata dukan kawo wuƙa sai an ƙwace ta amma hakan ba mai yowuwa bane domin kuwa shi faɗan da ya fi ƙarfinka wasa kake mayar da shi. A fili kuma sai ta nufi wajen nasu tana faɗin. "Sannu Mai Gari, sannu Salele, ashe kuma ku haka abu ya auku, kai amma matar nan tausayinta da sauƙi, dan rashin imani auran mijin maƙociya, sai da ta ga kun jigata babu mamora sannan ta ƙyale ku, amma matar nan ta iya ganganci haihuwa da damina, sai da ta mayar da ku akwai ya babu kakar wajen uba, sannan ta bar ku, haba ni fa in ce ashe shi ya sa na zo na gama burunkaɗuwar maganata har zan fita sai a sannan ta ganni, ashe dai lokacin da nake maganar ba ta ma san ina yi ba yo tana huce gajiyar da ta tarawa kanta, tabbas na yarda kowa da kiwon da ya karɓe shi wai maƙocin mai akuya ya sayi kura, amma kai dai Taju an yi shegen yaro, ai ni bata birgeni ba da bata maka ligigif ba, ai na so rigi-rigi ta maka yadda nan gaba ko amfanuwa ba za ka yi ba, haka kawai ka ɗakko mana mace tausayinta da sauƙi ka kawo mana gida, ga shi a rana ɗaya duk tana neman mayar da ku mata -maza, yo mata maza mana, yadda ta yi kalaci da ku, ku duka ukun ai ba ƙaramin nakasta ku ta yi ba" Gwaggo da take maganar ƙasa-ƙasa tamkar tana raɗa ta faɗa dan gudun kar ta ɗaga murya a yi rashin sa'a Lailar ta jiyo ta.Ta faɗa tana ɗora hannunta a kan hannun Mai Gari da ya yi lifet ya yi reran hannuwan nasa kowanne ya kalli nasa wurin da ban. "Ana tsoronka ɗan mayya, ya ce daga ni har uwata" Cewar Salele a zuciyarsa ganin yadda Gwaggon take magana tamkar an riƙe mata maƙoshi ita ala dole raɗa take ba ta so Laila ta ji. "Ramma, Ramma, Ramma" Mai Gari ya faɗa cikin muryarsa da ba ta fita sabo da wahalar da ya sha. "Na'am Mai Gari ka ganni a kusa da kai, sannu ka ji, sannu da dole, Allah sa zakkar jiki ne, wallahi ba zan ji haushinka ka ba, ai na san ba da son ranka ba ka aikata, dole uwar na ƙi aka maka, haka kawai, da na san abin da za ta aikata da tuni na dawo da wuri to sai dai a lokacin da mage take nan ɓera ba ya wasa, kuma dama ana marin mai rai ne dan matacce ya ji tsoro, dan dai hakan da ta yi ba abin ƙwarai bane tun da a yi a gama yau ya fi a ƙarasa gobe, kuma ni ma da kuke gani tun da na bar gidan nan, ba a hayyacina nake ba wallahi gamo muka yi dan ba na ce na yi ba tun da ba ni kaɗai ba ce, amma abin ba a cewa komai kuma da a ce INGOZOZANCIN nan ba gado bane wallahi da na watsar da shi daga yau, to amma abin sai ido bebiya ta auro makaɗi, amma kam tabbas yau na ga larura auren namiji da ƴaƴa. Sai dai na san komai nisan dare gari zai waye, kuma komai nisan jifa dole wata rana ya dawo ƙasa " Ta kai ƙarshen maganar tana sharɓar hawaye. "Gwaggo wai duk warin nan da ya ciki ɗaki yake neman sumar da mutane ke bakya ji?" Salele ya yi ƙarfin faɗar hakan ganin Gwaggo ta dage sai zuba take kamar bishiyar kanya. Hanci ta ɗaga sama, tana jan hancin wai ko za ta ji warin amma dai sai ba ta ji ba. "Allah sarki Salele yo dama ɗakin da aka aiwatar da saɓon Allah, mai zai yi ban da wari, to da yake ni hancin nawa duk mura ta ƙudundune shi, ban da zuba kamar hancin tinkiya babu abin da yake" Babu wanda ya sake cewa uffan Taju ya shiga ƙoƙarin tashi zaune, duk da yau ba ita ce rana ta farko ba da Laila ta taɓa yin tusa a kansa amma dai tabbas yau ya jigata fiye da tunanin mai tunani. Tun da yake ƙoƙarin tashi Gwaggo take aika masa harara kamar idanunta za su faɗo ƙasa, dan ta san hatta halin da gadon bayanta yake ciki na ƙagewa ta samu ne sanadin goyon Nasiru kuma duk Tajun ne ya jaza mata hakan dan haka a halin da ake ciki yanzu ji take tamkar ta samo kulki ta shiga dukansa tamkar an aiko ta. "Matso ki yi aikin lada Ramma, taimaka mini Ramma" Cewar Mai Gari da yake baza hannuwa shi a dole ta taimaka masa ya tashi zaune. "Kai gaskiya matar nan ta muku aika-aika ba aiki ba ma" Gwaggo ta faɗa cikin alhinin zaton ta na fyaɗe Laila ta musu, ba ta san cewa tarzomar sakin tusa a kan su ne kaɗai ya haifar da halin da suke ciki ba. Haka ta kama Mai Gari ta ɗaga shi da taimakon nata ya tashi zaune, har lokacin yana sakin numfarfashi tamkar wanda yake gargarar mutuwa. "Ramma, Ramma, Ramm" "Haba Mai Gari ya kake rafka mini kira kamar wani makaho bayan gani nan muraran a gabanka, kana gani to kiran kuma na mene ne kake yi tamkar za ka ari baki" "Ramma duba mini wuyan nan nawa ki gani, maƙogwarona yana wurin ko kuwa ya fincike" "Na dawo in ji ɗan yawon duniya, da tada zaune tsaye naman asalin amarya a wajen ɗaurin aure, yaya ana zancen fyaɗe kai amma ba ta jikin naka kake ba kar a je ma ko ta maka lahani amma kana zancen ko maƙogwaronka ya fincike sai ka ce kan keken ɗinki" Ta faɗa tana masa kallon mamaki ganin bai tanka mata ba ta sake cewa. "Ko dai mansileta za ka shafa ko ka ji dama-dama yo ai dama in lela ta ƙiya sai a koma caca" Gwaggo ta faɗa dan ita har yanzu ta ɗauka fyaɗe aka musu. "Kai amma gaskiya Gwaggo kin iya shiga shari ba shanu sai ka ce a shirin film za a ce an mana fyaɗe sai ka ce wasu mata, yo ai mace ce ake yi wa fyaɗe amma namiji kuwa fa, ko dan shi ma idan aka tirsasa shi duk ana kan hanyar cewa fyaɗen aka yi" Taju da yake gyara zamansa ya faɗa a ransa yana jiran yaga yadda doguwar diramar za ta kasance. "Ni dai na fi ji da maƙogwaron nawa, tun da daga nan nake samun haɗiyar abinci da ruwa, ki duba mini dan wallahi wajen muƙamuƙin nan nawa kamar ana yin faskare" Mai Gari ya faɗa yana miƙa hannu wajen saitin muƙamuƙin nashi yana nuna mata. "Ana maganar masarrafar aure, kai kana batun maƙogwaro" Gwaggo ya faɗa a zuciyarta. "Hatta kaina ma sai in ke jin kamar ya mugaɗe, fatana ɗaya kar in koma tamkar ɗan ruwan mai mogaɗaɗɗan kai" Ya faɗa cikin muryarsa da yake magana ba ta fita."Kai dai ana ga yaƙi kana ga ƙura, kai da ake maganar mafitsara amma kana maganar maƙoshi da maƙogwaro ko dai mai ɗungurugum ta muki ku haihuwa har hanji" Gwaggo ta faɗa tana kama haɓa. "Gwaggo duk wannan abin da kike faɗa fa ba shi da nasaba da abin da ya faru, ba wani abu bane fa illa zaman ƴan bori da ta yi a kawunanmu ta ringa sakin iskar tusa kamar an buɗe salansar babbar mota" Salele da ya yi nasarar samun tashi zaune ya faɗa yana ɗan yamutsa fuska jin duk wuyansa yana ciwo har kansa ma sarawa yake yi. "Zaman ƴan bori, yanzu sabo da kawai ta yi zaman ƴan borin a kan ku kuke wannan baloƙoƙon?" MAMAN AFRAH 09013181851 *Littafin Ungozoma 500 ne ga mai buƙata zai iya biyan 400 kafin mu gama free pages, za mu gama free pages a page 26 idan na gama free pages zai koma 500. Za a biya ta acc ɗin Fa'iza abubakar 9030283375 opay bank* shaidar biya ta 09013181851 [8/19, 17:57] Mom mashkur & Afrah: UNGOZOMA (Mai karɓar haihuwa) NA MAMAN AFRAH F.C.W GARGAƊI⚠️ Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ta kowace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowace kafa ba sai da izinina a kiyaye. Hadaddu Kuma ingantattun kayan gyaran gashin mamanzee(chebe hair set) Wadanda suke dawowa da martabar gashin Kai komai lalacewarsa biiznillahi Rabbi Ga kyau ga inganci ga saukin kudi muddin kika fara amfani da kayammu sekindawo Muna da kyakkyawan labari Kanki zeyi kyau yarika sheki yayi tsayi yayi laushi duk matsalar da ke cikin kanki zata kau in sha Allah Munada set complete Kuma Muna Bada pieces Haka Kuma Muna Bada Sari Muna turawa akowanne gari kike Kuma Ako wacce kasa kike Phone number 08079130166 Page 1️⃣7️⃣➡️1️⃣8️⃣ "Ikon Allah na zaune ya faɗi, ƙaran mene ne wannan kamar motar tan-tan ta wuce?" Gwaggo Ramma ta faɗa a zuciyarta gabanta yana matsanancin bugu tamkar ana bugawa da guduma. Cikin sanɗa ta fara lallaɓawa ta tura ƙofar ɗakin nata, ta shige tana shiga amma ganin kayan Laila a ɗakin ta hasken farin watan da ya haska ɗakin sai gabanta ya faɗi, cikin kiɗima ta juyo ta fito daga ɗakin dan ganin kayan ya ruɗa ta, domin hakan yana nuna mata kenan ɗakin ya zama mazaunin Laila kuma ita alal haƙiƙa ko ana ha maza ha mata babu abin da zai sa su haɗa ɗaki da wannan matar mai kamar dunƙulalliyar giwa. Duk da tunaninta bai bata ta tuna inda sauran mutanen gidan suke bare ma mai gayya mai aiki Laila, amma a haka ta yanke hukuncin shiga ɗakin Salele dan tana ganin can ɗin tamkar hanyar tsira ne, sai ma ta shiga tunanin cewa ƙaran da ta ji wataƙila ma kawai gizo ne kunnuwanta suke mata. Tana zuwa ƙofar ɗakin baram ta bankama kofar ta shige, hasken fitilar Laila da ke yashe a tsakar ɗakin shi ne ya sanya ta hangi Laila a zaune a kan wani abu wanda tunaninta bai kawo cewa mai gidanta Mai Gari ne da jikokinta ba, dan ita ganin Lailar ya sanya cikin inda-inda ta ce "Allahu akbar kabiran, shi ya sa aka ce tunani baiwa ne nutsuwa da hankali kuma aikin ƙwaƙwalwa ne, rashin sani ne wanda ya fi dare duhu, aradun Allah ranki ya daɗe ba nan na yi niyyar shigowa ba hasali ma ban san kina ɗakin nan ba ki mini afuwa ki yafe ni dan Allah da soyayyar ma'aikinsa kar ki bari allura ta tono garma, na san iya gani iya ƙalewa" Cewar Gwaggo tana ƙoƙarin juyawa za ta bar ɗakin dan tsabar ruɗewa ma bata lura da warin da ɗakin ya ɗumame ba ita kwanciyar hankalinta ɗaya ta bar ɗakin kar ta je Laila ta mata hukunci. Laila kuwa lokacin da Gwaggo take bayanin idanunta a rufe suke tana sauke lumfashi da sauri da sauri tamkar mai naƙudar da ta haihu yanzu, sabo da fitar tusar shi ne samun lafiyar ta da haka ba ta ma san abin da Gwagho take faɗa ba. "Ramma kin ganni manne da mazaunan ranta ya daɗe, tun ɗazu take sakin iska kamar tayar motar lodin shanu, in ban da ma duk nisan tashin tsuntsu sai sama ta ga bayansa ta yaya za a yi matar nan ta danne ni, take sakin iska a kaina ina Mai Gari, yau na tabbatar duk girman dutse bai kai ƙaramin goro amfani ba, amma dai yau na ga fallasa auren bashi domin kuwa wayon a ci ne ya sa aka kori kare daga bakin ɗinya" Cewar Mai Gari a zuciyarsa yana danne hawayen da ke ƙoƙarin kwaranyo masa dan shi haƙiƙa ya san alhakin mutane ne da suke ɗauka, ya sa Allah ya kawo matar nan take azabtar da su. "Gwaggo kin gammu nan fa daga Malam har ni da kuma Taju muna karɓar gashin ƙuma, lallai ba a yi wa uwar kwarto gorin ɗa, ko ba jima ko ba daɗe sai ya dire mata nashi" Salele ma ya faɗa a ransa yana jin nauyin Laila tamkar an ɗora musu duron ruwa. Gwaggo kuwa ko waiwaye ba ta yi ba, ta juya ta nufi bakin ƙofa za ya fice daga ɗakin, har zaninta yana kuncewa tana kamowa ta riƙe da hannu ɗaya dan ɗaya hannun kayan aikin INGOZOMANCIN ta ne. "Ina za ki je kuma" Ta tsinkayi muryar Laila a kunhuwanta tana dab da fita daga ɗakin" Wani uban birki Gwaggo ta ja tamkar motar da ta kusa faɗawa kwalbati. Laila kuwa lokacin da ta daddage ta tashi tsaye domin kuwa ta gama yin abin da ya kawo ta, tashin ta ke da wuya ta hangi Gwaggo tana shirin fita daga ɗakin, dan ita har ga Allah ba ta san Gwaggo ta shigo ba ma. "Dama yaron albarka na kawo miki, wannan yaro mai ɗan karen kirki ko nauyi bashi da shi shafalfal tamkar na goyi leda, ga shi tun da muka je har na karɓi haihuwar nan ko kuka bai yi ba yana ta baccinsa" Gwaggo ta samu kanta da faɗar hakan dan maganar da Laila ta yi ya nuna mata ba ta ma ji abin da ta faɗa ɗazu ba. "Zan sakko" Cewar Nasir da ya tashi daga bacci yanzu. "Ka ga ɗan halak ya ƙi ambato, ashe ma kana kan hanyar tashi daga bacci ni duk tunanina ma baka tashi ba" Gwaggo ta faɗa, kai da ka ganta ka san babu nutsuwa a tare da ita, dan dama har yanzu bata gama dawowa hayyacinta ba daga abin da jaririn gidan Malam Mammani ya musu ba yanzu kuma ta dawo ta tarar da wani sabon salo wai kiran sallah da usur, Dariyar yaƙe ta saki dan ita kwata-kwata ta ƙi jinin haɗa hanya da Laila ko da kuwa ta magana ce, "Mu je ɗakina ki sauke shi" Tun kan Laila ta rufe bakinta Gwaggo ta juya cikin sauri ta fita duk da bata san ma ina ne ɗakin na Laila ba amma dai tun da ta san iya ɗakuna biyu ne a gidan to kuwa kenan ɗakin ita Gwaggon shi ne a matsayin ɗakin da Laila ta ɗauka a matsayin nata. "To ni ƴasu yanzu a ina zan ke kwana ni Ramma, ba dai nufin matar nan ba a ɗaki ɗaya za mu zauna ni da ita tun da mu biyu ne mata ni da ita, haka kawai in je in ke shiga uku da abubuwan da za ta ke mini ko kuwa dai manufarta mu kwatsu a ɗaki laya da Salele da Mai Gari da Taju sai ka ce a gidan arna" Gwaggo ta jefawa kanta tambayar a zuciyarta, sai dai ba ta buƙatar amsa yanzu kuma abin da take so bai wuce ta sauke yaron daga bayanta ba. "Ki kai wa mijinki da jikokin ki taimakon gaggawa" Cewar Laika cikin halin ko in kula tana zaunawa a bakin gadon Gwaggo wanda ya bada saurin " ƙiƙar". "To,to,to" Gwaggo ta faɗa dan son ganin an zauna lafiya, amma ba ta fahimci komai ba a maganar sai dai ta shiga ruɗani jin ta ce a kai musu taimakon gaggawa zuciyarta ba ta barta da tunanin abin da ya samu su Mai Gari da su Salelen ba. Tana fitowa daga ɗakin ta sunkuya a waje tana danna bayanta da hannunta jin wata irin gajiya ta riƙe mata gadon baya, ba komai bane kuwa ya kawo hakan ba sai goyon Nasiru. Tana cikin hakan sai ta fara jiyo ana tari, ana kuma sakin wani nishi daga ɗakin Salele lamarin da ya ƙara jefa kwanyarta a kogin tunanin dan ita dai ba ta ga kowa a ɗakin ba hasali ma ta ɗauka ko su Mai Gari bayan ɗakuna Lailar ta mayar da su. Da ɗan sarsarfa ta nufi ɗakin tana shiga lokacin Salele ya miƙa hannu dakyar ya kunna fitila amma har lokacin babu wanda ya yi wani ƙwaƙƙwaran motsi, sun yi lifet a tsakar ɗakin. Salati Gwaggo ta shiga rattabowa sabo da tunaninta sai ya bata cewar Laila fyaɗe ta yi wa maza guda uku, wato ta tirsasa su suka yi tarayya da ita hakan ya sanya ta ji kishin Mai Gari ya turnuƙe mata zuciya dan ita akwai kishi hakan ne ma ya sanya ba ta son Mai Gari ko da wasa ya raɓi wata mace, amma sai gashi yau a aikin banza a sadaka wata ta zo ta yi mu'amala da mijinta, a gefe guda kuma tana tausayin Salele amma ko kaɗan ba ta ji tausayin Taju ba dan tana ganin shi ya jaza musu halin da suke ciki, domin shi ya kawo musu Laila gida kuma dama ai duk tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa kan duka. "La'ilaha illallahu, muhammadur rasulullahi S.A.W, ni Ramma yau na ga ɗan jijjiɓin hau zalla, yanzu shirmemiyar matar nan ta haike muku ku duka uku rigis sai ka ce ta samu wasu agwagi, fisabilillahi ina laifin ma ta samu ɗan maraƙe (Namijin saniya) Ko dai ta samu (Doki) Ai su ne daidai da ita amma ba mutane ba, yo ina dalili ina ɗan mafari wane ɗan adam ne zai iya da wannan mata, amma dan wulaƙanci gaida sirika da mazaunai shi ne ta zo har da Mai Gari ta haikewa gashi na sai nishi yake kamar an lodowa jaki kaya, to ƙur'anin Allah sai in ja carbi mai dubu in karanta mata addu'ar da za ta saka matantakar ta(HQ) Ta manne tamkar an saka ruwan dalma an rufe tillar kwanon silba, ko wurin ya koma kamar an saka sufagilu an nane kai ko ma wurin ya ɓace ɓat ta neme shi ta rasa dan gani za ta yi babu ƙofar babu dalilinta, in ga nan gaba da wane wurin za ta yi wa wasu fyaɗe" Gwaggo ta faɗa a zuciyarta tana jin kamar ta koma ta shaƙe Laila a kan wannan tozarci da ta yi ko ma ta mata dukan kawo wuƙa sai an ƙwace ta amma hakan ba mai yowuwa bane domin kuwa shi faɗan da ya fi ƙarfinka wasa kake mayar da shi. A fili kuma sai ta nufi wajen nasu tana faɗin. "Sannu Mai Gari, sannu Salele, ashe kuma ku haka abu ya auku, kai amma matar nan tausayinta da sauƙi, dan rashin imani auran mijin maƙociya, sai da ta ga kun jigata babu mamora sannan ta ƙyale ku, amma matar nan ta iya ganganci haihuwa da damina, sai da ta mayar da ku akwai ya babu kakar wajen uba, sannan ta bar ku, haba ni fa in ce ashe shi ya sa na zo na gama burunkaɗuwar maganata har zan fita sai a sannan ta ganni, ashe dai lokacin da nake maganar ba ta ma san ina yi ba yo tana huce gajiyar da ta tarawa kanta, tabbas na yarda kowa da kiwon da ya karɓe shi wai maƙocin mai akuya ya sayi kura, amma kai dai Taju an yi shegen yaro, ai ni bata birgeni ba da bata maka ligigif ba, ai na so rigi-rigi ta maka yadda nan gaba ko amfanuwa ba za ka yi ba, haka kawai ka ɗakko mana mace tausayinta da sauƙi ka kawo mana gida, ga shi a rana ɗaya duk tana neman mayar da ku mata -maza, yo mata maza mana, yadda ta yi kalaci da ku, ku duka ukun ai ba ƙaramin nakasta ku ta yi ba" Gwaggo da take maganar ƙasa-ƙasa tamkar tana raɗa ta faɗa dan gudun kar ta ɗaga murya a yi rashin sa'a Lailar ta jiyo ta.Ta faɗa tana ɗora hannunta a kan hannun Mai Gari da ya yi lifet ya yi reran hannuwan nasa kowanne ya kalli nasa wurin da ban. "Ana tsoronka ɗan mayya, ya ce daga ni har uwata" Cewar Salele a zuciyarsa ganin yadda Gwaggon take magana tamkar an riƙe mata maƙoshi ita ala dole raɗa take ba ta so Laila ta ji. "Ramma, Ramma, Ramma" Mai Gari ya faɗa cikin muryarsa da ba ta fita sabo da wahalar da ya sha. "Na'am Mai Gari ka ganni a kusa da kai, sannu ka ji, sannu da dole, Allah sa zakkar jiki ne, wallahi ba zan ji haushinka ka ba, ai na san ba da son ranka ba ka aikata, dole uwar na ƙi aka maka, haka kawai, da na san abin da za ta aikata da tuni na dawo da wuri to sai dai a lokacin da mage take nan ɓera ba ya wasa, kuma dama ana marin mai rai ne dan matacce ya ji tsoro, dan dai hakan da ta yi ba abin ƙwarai bane tun da a yi a gama yau ya fi a ƙarasa gobe, kuma ni ma da kuke gani tun da na bar gidan nan, ba a hayyacina nake ba wallahi gamo muka yi dan ba na ce na yi ba tun da ba ni kaɗai ba ce, amma abin ba a cewa komai kuma da a ce INGOZOZANCIN nan ba gado bane wallahi da na watsar da shi daga yau, to amma abin sai ido bebiya ta auro makaɗi, amma kam tabbas yau na ga larura auren namiji da ƴaƴa. Sai dai na san komai nisan dare gari zai waye, kuma komai nisan jifa dole wata rana ya dawo ƙasa " Ta kai ƙarshen maganar tana sharɓar hawaye. "Gwaggo wai duk warin nan da ya ciki ɗaki yake neman sumar da mutane ke bakya ji?" Salele ya yi ƙarfin faɗar hakan ganin Gwaggo ta dage sai zuba take kamar bishiyar kanya. Hanci ta ɗaga sama, tana jan hancin wai ko za ta ji warin amma dai sai ba ta ji ba. "Allah sarki Salele yo dama ɗakin da aka aiwatar da saɓon Allah, mai zai yi ban da wari, to da yake ni hancin nawa duk mura ta ƙudundune shi, ban da zuba kamar hancin tinkiya babu abin da yake" Babu wanda ya sake cewa uffan Taju ya shiga ƙoƙarin tashi zaune, duk da yau ba ita ce rana ta farko ba da Laila ta taɓa yin tusa a kansa amma dai tabbas yau ya jigata fiye da tunanin mai tunani. Tun da yake ƙoƙarin tashi Gwaggo take aika masa harara kamar idanunta za su faɗo ƙasa, dan ta san hatta halin da gadon bayanta yake ciki na ƙagewa ta samu ne sanadin goyon Nasiru kuma duk Tajun ne ya jaza mata hakan dan haka a halin da ake ciki yanzu ji take tamkar ta samo kulki ta shiga dukansa tamkar an aiko ta. "Matso ki yi aikin lada Ramma, taimaka mini Ramma" Cewar Mai Gari da yake baza hannuwa shi a dole ta taimaka masa ya tashi zaune. "Kai gaskiya matar nan ta muku aika-aika ba aiki ba ma" Gwaggo ta faɗa cikin alhinin zaton ta na fyaɗe Laila ta musu, ba ta san cewa tarzomar sakin tusa a kan su ne kaɗai ya haifar da halin da suke ciki ba. Haka ta kama Mai Gari ta ɗaga shi da taimakon nata ya tashi zaune, har lokacin yana sakin numfarfashi tamkar wanda yake gargarar mutuwa. "Ramma, Ramma, Ramm" "Haba Mai Gari ya kake rafka mini kira kamar wani makaho bayan gani nan muraran a gabanka, kana gani to kiran kuma na mene ne kake yi tamkar za ka ari baki" "Ramma duba mini wuyan nan nawa ki gani, maƙogwarona yana wurin ko kuwa ya fincike" "Na dawo in ji ɗan yawon duniya, da tada zaune tsaye naman asalin amarya a wajen ɗaurin aure, yaya ana zancen fyaɗe kai amma ba ta jikin naka kake ba kar a je ma ko ta maka lahani amma kana zancen ko maƙogwaronka ya fincike sai ka ce kan keken ɗinki" Ta faɗa tana masa kallon mamaki ganin bai tanka mata ba ta sake cewa. "Ko dai mansileta za ka shafa ko ka ji dama-dama yo ai dama in lela ta ƙiya sai a koma caca" Gwaggo ta faɗa dan ita har yanzu ta ɗauka fyaɗe aka musu. "Kai amma gaskiya Gwaggo kin iya shiga shari ba shanu sai ka ce a shirin film za a ce an mana fyaɗe sai ka ce wasu mata, yo ai mace ce ake yi wa fyaɗe amma namiji kuwa fa, ko dan shi ma idan aka tirsasa shi duk ana kan hanyar cewa fyaɗen aka yi" Taju da yake gyara zamansa ya faɗa a ransa yana jiran yaga yadda doguwar diramar za ta kasance. "Ni dai na fi ji da maƙogwaron nawa, tun da daga nan nake samun haɗiyar abinci da ruwa, ki duba mini dan wallahi wajen muƙamuƙin nan nawa kamar ana yin faskare" Mai Gari ya faɗa yana miƙa hannu wajen saitin muƙamuƙin nashi yana nuna mata. "Ana maganar masarrafar aure, kai kana batun maƙogwaro" Gwaggo ya faɗa a zuciyarta. "Hatta kaina ma sai in ke jin kamar ya mugaɗe, fatana ɗaya kar in koma tamkar ɗan ruwan mai mogaɗaɗɗan kai" Ya faɗa cikin muryarsa da yake magana ba ta fita."Kai dai ana ga yaƙi kana ga ƙura, kai da ake maganar mafitsara amma kana maganar maƙoshi da maƙogwaro ko dai mai ɗungurugum ta muki ku haihuwa har hanji" Gwaggo ta faɗa tana kama haɓa. "Gwaggo duk wannan abin da kike faɗa fa ba shi da nasaba da abin da ya faru, ba wani abu bane fa illa zaman ƴan bori da ta yi a kawunanmu ta ringa sakin iskar tusa kamar an buɗe salansar babbar mota" Salele da ya yi nasarar samun tashi zaune ya faɗa yana ɗan yamutsa fuska jin duk wuyansa yana ciwo har kansa ma sarawa yake yi. "Zaman ƴan bori, yanzu sabo da kawai ta yi zaman ƴan borin a kan ku kuke wannan baloƙoƙon?" MAMAN AFRAH 09013181851 *Littafin Ungozoma 500 ne ga mai buƙata zai iya biyan 400 kafin mu gama free pages, za mu gama free pages a page 26 idan na gama free pages zai koma 500. Za a biya ta acc ɗin Fa'iza abubakar 9030283375 opay bank* shaidar biya ta 09013181851 [8/19, 17:57] Mom mashkur & Afrah: UNGOZOMA (Mai karɓar hihuwa) NA MAMAN AFRAH F.C.W GARGAƊI⚠️ Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ta kowace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowace kafa ba sai da izinina a kiyaye. Ina mata ƴan ƙwalisa, babbar mace alkyabbar mata, macen mai gyara ita wacce ta isa da miji su o'o sai dai su ga ƙeyar mijinta idan ya wuce amma basu ishe shi kallo ba domin babu abin da za su nuna mata. Gyaran gashi babbar martaba ce da take ɗaga darajar mace, musamman kayan gyaran gashin MAMAN ZEE da ya yi fice a ko ina ake labarinsa. Gani ya kori ji sai an gwada akan san na ƙwarai siyan na gari mayar da kuɗi gida💃💃💃💃💃💃💃💃 Hadaddu Kuma ingantattun kayan gyaran gashin mamanzee(chebe hair set) Wadanda suke dawowa da martabar gashin Kai komai lalacewarsa biiznillahi Rabbi Ga kyau ga inganci ga saukin kudi muddin kika fara amfani da kayammu sekindawo Mana da kyakkyawan labari Kanki zeyi kyau ya rika sheki yayi tsayi yayi laushi duk matsalar da ke cikin kanki zata kau in sha Allah Munada set complete Kuma Muna Bada pieces Haka Kuma Muna Bada Sari Muna turawa akowanne gari kike Kuma Ako wacce kasa kike Phone number *08079130166* Page1️⃣9️⃣➡️2️⃣0️⃣ *MALAM MAMMANI* Da rarrafe Malam Mammani ya iya tahowa daga ɗakin, rarrafan ma dakyar yake iya jan gwiwarsa dan duk ya ruɗe da ganin wannan ibtila'in. Yana zuwa falon yake jin ƙaran nishi-nishi a bayansa alamar ana binsa ɗif ya yi ya tsaya a da rarrafan dan cikinsa har ya murɗa masa dan tunani ɗaya ne ya fara zuwa masa, na ɗayan biyu ko dai gawar ce take biye da shi ko kuma jaririn ne ya sake fitowa daga cikin zai masa taƙidaranci. Daga inda ya tsaya bai motsa ba sai bakinsa da yake ta kai kawo da shi kansa bai san abin da yake furtawa ba ga uwa uba ruɗanin da ya baibaye shi dan ya kasa juyawa bare ya tabbatar da abin da yake biye da shi. A take ya samu nasarar fara jero kalmar shahada domin samun ya cika da imani dan a ransa ya fara tunanin ajalinsa ne zai sauka, dan jira kawai yake ya ji gawar ko jaririn ya damƙi wuya ko bayansa. Jin motsin da nishin ya matso daf da shi sai ya ji kamar ya zura da gudu ya tsira amma ina! Ya san gwiwa da hannunsa ba za su bashi damar hakan ba dan ba ya jin ƙarfin ko misƙala zarratin da har zai iya taɓuka wani abu. Ta wutsiyar ido ya fara ɗan kallon saitin bayansa cikin firgici tunanin abin da zai je ya zo wanda zai yi tozali da shi, sai dai ganin Kaka tana rarrafowa daga ita sai ɗan tofi (Siket ɗinsu na tsofaffi) Zaninta kuwa yana rataye a wuyanta kamar wacce za ta filin daaga, tana nishi tamkar wacce aka ɗorawa ƙaton dutse a ƙirji. Wani takaici ne ya mamaye zuciyar Malam ganin ashe dai babu ɗaya daga cikin abin da yake tsammanin ya biyo shi wato gawa ko jaririn sai kawai ya ji saukar wata ajiyar zuciyar mai ƙarfi wacce bai san daga ina take ba. "Haba Kaka yanzu haka za ki fito ki bar gawar ita kaɗai, ai sai ki zauna a ɗakin" Malam ya samu kansa da furtawa yana mayar da kallonsa kan Kaka da ta yi wurjanjan duk da shi ma ya san da zai duba mudubi tabbas a wurjanjan ɗin zai ga kansa domin ya san sai ya ga kansa tamkar wanda ya kuɓuto daga bakin kura saboda yadda yake a tsorace. Kaka ba ta ce masa ko ƙala ba haka ta cigaba da rarrafowa sai da ta zo ta ɗan gota shi kaɗan, sannan ta dakata tana ɗan jan ɗan tofinta ta gyara in da ta ji ya tattare, ta sakko zaninta daga wuyanta ta ɗaure a tsantsa sannan ba tare da ta ko kalli inda Malam ɗin yake ba cikin rawar murya ta ce. "An ƙi a zauna da gawar idan gawar ubana ce, haka kawai kai da kake mijin gawar kuma uba ga jaririn baka tsaya ba ka gudo sai ni da babu abin da ya haɗa ni da jaririn uwarsa ce kawai take jikata sai na tsaya na halaka a ban... "Dukan ku, ku dakata!" Muryar jaririn nan ta faɗa daga can cikin ɗakin har wani amsa amo take hakan ne ya dakatar da Kaka daga maganar da take wanda tsabar ruɗewa har ta yi gaba da rarrafen za ta fice sai kuma cikin kiɗima ta dawo ta tsaya a kan gwiwoyinta a inda take da ta tuna an ce a dakata. Malam Mammani kuwa idanu ya zaro cikin firgici sai hannu ya kai ya zaro tazugen wandonsa daga cikin wandon da sauri ya ɗaura a tsantsa dan cikin ruɗu ya fara tunanin ko dai zanin da Kaka ta ɗaura zai sa jaririn ya bar ta ta tafi shi ya sa shi ma ya yi hakan dan ya tsira da ransa. jin wurin da tazugen bai hau ka ba a wandonsa nasa yana saɓulewa yana neman yin tsirara a gaban Kaka duk da ita ma kusan a tsirarar take dan daga ita sai ɗan tofi ya kamo wurin ya ƙudundune ya cusa a jikin tazugen cikin zafin nama ya cigaba da rarrafawa dan so yake ya fice daga ɗakin tun da dai ya tabatar da a kan idanunsa jaririn yana cikin gawar kafin dai ya fito shi ya fice. Kaka ganin ya gifta fa zai fice ya barta ita kaɗai ta miƙa hannu ta kamo rigarsa ƙiiii ta dawo da shi saitin in da take tana aika masa hararar ka yi kaɗan. Kallonta Malam ya yi kamar ya saki kuka dan takaici amma babu yadda ya iya haka shi ma ya dakata. "Wai dan taurin kai fita za ka yi? To kana zuwa waje za ka ganka ka dawo cikin ɗakin" Muryar jaririn ta ƙara faɗa cikin amsa kuwwa, Malam cikin sauri ya fara girgiza kansa alamar a'a. " Za ku tafi amma da sharaɗin duk wanda cikin ku ya kuskura ya furta wani abu daga cikin abin da ya faru to ya sani zai dawo cikin gawar nan ne a binne mu tare" "Babu mai ji" Malam da Kaka suka haɗa baki wajen faɗa. "Dan haka kar wanda ya razana ko nuna wata alama ta tsoro ku yi tamkar babu abin da ya faru kuma kowanne ya tashi ya kunce ɗaurin tsantsar da ya yi ku fita a nutse" Ana gama faɗar hakan suka ji tamkar an yi ruwa an ɗauke babu maganar jaririn da sauri suka tashi tsaye ƙafafun kowanne suna karkarwa kowa ya shiga ƙoƙarin saita kansa, Kaka baya ta juya wa Malam ta kunce zaninta ta ɗaura a kan ɗan tofinta shi ma da sauri ya sunce tazugen ya ƙara ɗaurawa akan wandon nasa yadda babu wanda wanda zai lura cewa tazugen ba a cikin wandon yake ba dan bashi da nutsuwar saka tazugen a mazagin wandon. Haka suka fito tsakar gidan Kaka ta shiga salallami tare da sakin kukan mutuwar jikar tata, kishiyoyin murna fal ransu amarya ta mutu shikenan sun huta, Malam ya daina nuna rawar ƙafa a kan ta. Haka aka taru ana nuna al'ajabin mutuwar uwar gidan Malam ɗin da mai ɗakin tsakiya Kaka ta ce su zo su taimaka mata shi kuma Malam ɗin ya tafi gidan su Shamsiyyar ya sanar da mutuwar ta. Kaka a tsorace take dan haka da aka shigo ɗakin ma dai kaffa-kaffa take dan hatta kukan mutuwar da take matsowa take dan tamkar ka ce kamota ta zura da gudu haka ta yi. Ganin Talatuwar tana motsa ƙafa hakan ya sanya ɗaya daga cikin matan ta ce suma ta yi haka suka shiga nuna murna amma ta ciki na ciki dan sun so mutuwa ta yi ba suma ba, amma Kaka a tsorace take dan bata yarda cewa farfaɗowa ta yi ba gani take jaririn ne yake son ƙara dagula musu lissafi. Sai dai ganin ta buɗe idanunta tana magana a hankali hakan ya sanya Kaka ta ji dama-dama wai kibiya a ido. Tana farfaɗowa tamkar ta farfaɗo da naƙudar mai ƙarfi sai haihuwa gadan-gadan jaririya ta faɗo, Kaka ganin haka sai ta hau murna ta manta da damuwar da take ciki. Ƙarfin gwiwar da ta samu ganin yaron ba namiji bane. Haka kishiyoyin suka shaƙi takaici, Malam da ya kira ƴan uwan Talatuwa suka zo da kuka ganinta ta farfaɗo har da jaririyarta sai suka juya akalar kukan nasu da dariya da murnar farinciki. Malam ma haka yake yaƙen ganin matar tashi da jaririyar sai dai kuma bai ji shakkun haihuwar ba tare da UNGOZOMA Gwaggo ba, dan ya san yanzu ko da kuɗi aka kira ta ba za ta dawo ba. *GWAGGO RAMMA* Duk labarin dannewar da Laila ta musu da suka shiga bata labari sai ta yi kunnen uwar shegu da su ta nuna abin ma ba wani abu bane kuma ba shi da wani muhimmanci, dan tana ganin ita irin badaƙalar da suka sha ita da su Malam Mammani su Mai Gari ko hanyar basu bi ba. Sai dai tsoron abin da zai je ya zo ya sanya ta kama bakinta ta yi gum ba ta basu labari ba. Su Mai Gari kuwa haka kowa ya kama wurin kwanciya ya kwanta, Salele da Gwaggo suna ta yi wa Taju masifa a kan kawo musu Laila gida dan suna ganin gashi nan ko kwana ɗaya ba a yi ba suna karɓar hukunci. Gwaggo ban da tsaki kamar wata tsaka babu abin da take yi, dan shafalfalar katifar Salele ta ƙwace ta hau tare da ɗaukan zaninta a cikin kayanta da Laila ta sanya aka kawo aka jibge mata a ɗakin ta duƙunkune ƙafafu ta shiga sakin munshari. Mai Gari ma baccin ne ya sace shi dan sai rubda ciki ma ya yi ya ɗora haɓarsa dan ba zai iya kwantawa da gefen fuskarsa ba sabo da yadda gefe da gefen yake masa ciwo haka dai baccin wahala ya yi awon gaba da su duka har Taju kowa ya kama nasa wajen. Cikin bacci Gwaggo Ramma ta ji kamar ana ɗan jan zanin da ta rufa da shi, jin sanyi yana ratsata sai ta miƙa hannu ta ja zanin ta ƙara rufa har lokacin idanunata a rufe, ƙara janye mata zanin aka yi wannan karon sai ta ji gaba ɗaya zanin aka janye aka bar ta sanyi yana surar jikinta. Idanu ta buɗe ta laluma ta ga babu kowa ko alamar mutum sai ma ƙaran munsharin su Mai Gari da ya cika ɗakin, zanin ta ja ta rufa dan sai ta ɗauka a cikin bacci ne kawai ba wai jan zanin ake yi ba. Baccin ta cigaba da yi cikin kwanciyar hankali, can cikin baccin ta ji an kamo zanin da yake ɗaure a jikinta, hannu ta kai ta fisga ai kuwa aka ƙara kamo wajan da ta ɗaura zanin. "Na shiga uku ni Ramma, mene ne wannan ɗin kamar almara, kar dai ɗaya daga cikin yaran nan ne Salele ko Taju suke son su farmini tsakar daren nan, dama in banda jalala ƙwacen kwanan kishiya ta yaya za a haɗa ni ɗaki ɗaya kwana da garadan samarin zamani su rasa wacce za su nemi farwa sai ni uwar gyatumar su" Gwaggo ta faɗa a ranta gabanta na tsananta faɗuwa. Jin ana neman since zanin da ƙarfi ta kai wa hannun da ake neman mana tsirarar ai kuwa cikin sa'a ta kamo hannun sai dai abin mamaki wai ganin siriki a kan gadon matar ɗansa, sai ta ji hannun da ta kama ɗin ɗan ƙarami ne tamkar sillan kara mulmulawa ta yi ai kwa sai ta ji wani lagafgaf cikin mamaki ta ɗan ƙyallara ido ɗaya dan ganin wane irin hannu ne dan jin ƙanƙantar hannun ya sanya ta daina zargin su Taju. "Ha hayyu ya qayyumu" Cewar Gwaggo Ramma a zuciyarta gabanta tana faɗuwa da ƙarfi, domin abin da ta hango daga cikin idon da ta ƙyallara ya mugun ɗaga mata hankali tana ƙoƙarin tashi sai ta kasa ko da kataɓus. "UNGOZOMA, kin manta baki yanke mini cibiyar ba" Cewar jaririn nan da suka yi arangama da shi a gidan Malam Mammani. Idanun ta mayar ta runtse da ƙarfi tana fatan Allah sa a cikin mafarki ne. "Kin binne uwar" Ya faɗa cikin muryar ƴar ƙarama kuma cikin raɗa da alama ma ita kaɗai ce take jin maganar. "Wayyo Allah, ni ina ganin na baro ka a can gidan ashe dai ka biyo ni nan ɗin ma kenan tahowar tawa ya zama duk ɗaya wai an ce da karuwa hayo gado. Hannun da ya ɗora mata cibiyar jikinsa ta ɗaga ta warɓar gefe, dungurawa ta yi cikin azama ta bar shi a kan katifar da rarrafe take tafiya taa fatan ta samu mafaka a wajan Mai Gari ko ma mene ne ya same su tare. Da yake a gigice take sai ta faɗa kan Salele da yake baccinsa mai nauyi, cikin abin rufarsa ta shige ta maƙalƙale shi gabanta yana faɗuwa. Salele kuwa bai ma san ana yi ba wai kunu a maƙota dan haka baccinsa yake hankali kwance. Hannu Gwaggo ta kai za ta ƙanƙame Salele duk a tunaninta Mai Gari ne, a tsakiyar kansa wanda ya tara suma ta yi wa hannunta masauki wani irin ɗebe wuta Gwaggo ta yi tana karanto salatin annabi a zuciyar ta dan ta san dai duk firgicewar da za ta yi to kuwaba za ta kasa shaida kan Salele ba bare kuma kan Mai Gari mijinta da wanzami yake salsalewa tas da aska ko ɗigon gashi ba a bari. Da sauri ta janye hannun ta bankaɗo abin rufar ta tashi zaune. "Allah ka mini aikin gafara ni Ramma, ina zan kai abin kunyar nan idan aka kama ni kwance da jikana kuma na san mutane duk bayanin da zan musu ba za su fahimce ni ba Allah na tuba ko giyar wake na sha, mai zan yi da wani Salele" Ta faɗa tana taɓe baki kamar an ce ta duba gefenta ai kuwa sai ganin jaririn nan ta yi a tsugunne. Wani yawu ta haɗiye tana jin wani mugun tsoro yana dirar mata, kafin cikin sanɗa ta fara jan mazaunai domin neman in da za ta ɓuya. Ganin kamar abin ba zai mata ba sai ta fara mirginawa daga kwancen, cikin azama ta samu nasarar afkawa cikin abin rufar Taju, har lokacin a zaton ta Mai Gari ne hallaw. Garin ƙanƙame Taju ta taɓo belt ɗin da take jikinsa da ya yi ɗamara da ita. "Hasbunallahu wa ni'imal wakil, ni Ramma mai ya same ni yau daga in shiga bargon wannan sai in fito in shiga na wannan kuma har yanzu ban dace da samun bargon Mai Garin ba, haka kawai na ji hannuna ya taɓo zanzaro (Belt) Ban da Allah ya taimake ni yaran nan suna bacci mai nauyi ai da Taju sai ya ce wani abu na zo nema a wajansa yo ko bai faɗa da gaske ba ya faɗa da wasa dan ya bani kunya" Ta faɗa tana yayyace lulluɓin ta fito daga can gefe ta hangi mutum ya yi goho wanda take kyautata zaton Mai Gari ne dan dama ta dai san su kaɗai ne a ɗakin. Wurinsa ta nufa ganin jaririn ya rarrafo yana bin ta duk in da ta yi, Mai Gari kuwa shi sabo da yadda gefen fuskarsa yake masa raɗaɗi shi ya sa sai kawai ya yi goho haɓarsa a ƙasa a haka yake baccin. Gwaggo tana ƙarasawa wajansa da rarrafe waiwayawar da za ta yi don ta hango jaririn sai kuwa ta hango shi ya kusa ƙarasowa wajan da baya-baya ta fara ja ba ta san ta ƙarasa in da Mai Gari yake ba dan haka tana zuwa sai ta bangaji Mai Gari da yake durƙushe ya yi goho yana baccin wahala dan babu jin daɗi a baccin nasa ko kaɗan. Mai Gari jin an bangaje shi dama ba wani dogon bacci ya yi ba jin an warɓar da shi daga gohon ya faɗi wacakar sai tunaninsa ya tafi cewar Laila ce wata tusar ta matso ta shi ne ta ƙara dawowa za ta yi tusar a kansa. "Ya Allah ka mini alam nashra lakasadarak, Allah mugun ji mugun gani Allah ka kare mu" Mai Gari ya fara rattabo addu'o'in a zuciyarsa wasu ƙwallar tausayin kansa yana gangaro masa dan ya san tabbas ya zama abin tausayi in ma bai zama gawa ba matuƙae dai Laila ta ƙara yin zaman cin tuwo a kansa. MAI BUƘATAR UNGOZOMA ZAI BIYA 400 KAFIN MU GAMA FREE PAGES ZA MU GAMA FREE A PAGE 26 IDAN MUKA GAMA 500 NE. ZA A BIYA TA ASUSUN FAIZA ABUBAKAR 9030283375 opay SHAIDAR BIYA TA 09013181851 I [8/19, 17:57] Mom mashkur & Afrah: UNGOZOMA (Mai karɓar haihuwa) NA MAMAN AFRAH F.C.W GARGAƊI⚠️ Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ta kowace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowace kafa ba sai da izinina a kiyaye. Ina mata ƴan ƙwalisa, babbar mace alkyabbar mata, macen mai gyara ita wacce ta isa da miji su o'o sai dai su ga ƙeyar mijinta idan ya wuce amma basu ishe shi kallo ba domin babu abin da za su nuna mata. Gyaran gashi babbar martaba ce da take ɗaga darajar mace, musamman kayan gyaran gashin MAMAN ZEE da ya yi fice a ko ina ake labarinsa. Gani ya kori ji sai an gwada akan san na ƙwarai siyan na gari mayar da kuɗi gida💃💃💃💃💃💃💃💃 Hadaddu Kuma ingantattun kayan gyaran gashin mamanzee(chebe hair set) Wadanda suke dawowa da martabar gashin Kai komai lalacewarsa biiznillahi Rabbi Ga kyau ga inganci ga saukin kudi muddin kika fara amfani da kayammu sekindawo Mana da kyakkyawan labari Kanki zeyi kyau ya rika sheki yayi tsayi yayi laushi duk matsalar da ke cikin kanki zata kau in sha Allah Munada set complete Kuma Muna Bada pieces Haka Kuma Muna Bada Sari Muna turawa akowanne gari kike Kuma Ako wacce kasa kike Phone number *08079130166* Page2️⃣1️⃣➡️2️⃣3️⃣ Gwaggo hannu ta saka a cikin mayafin da ya rufe kansa ta sanya hannu ta rafko kan Mai Gari da ya sha aski rantal ta shiga murzawa tana murtsukawa tamkar tana shafa masa mai, Mai Gari shi duk tunaninsa Laila ce take son samun saitin in da za ta zauna ta saki iskar tusar ta kamar wata bodara. "Wayyo Allah, ki yi wa Allah Laila kar ki saki iskar nan a tsakiyar rantal ɗin nan nawa, aradu ina ga kan nan nawa zai iya tsagewa saboda ƙaran tusarki" Ya faɗa a zuciyarsa yana jin kamar ya kamo ta ya yi ta duka. Gwaggo jaririn ne ya yi tsalle ya sauka a kan cinyarta dan haka sai ta muskuta cikin tsoro ta yi zaman ƴan bori a kan ƙafafuwan Mai Gari da yake yashe a gefe fuskarsa har lokacin rufe da mayafin da ya rufa. Jin Gwaggo ta faɗa kan ƙaffafunsa, da duk tunaninsa Laila ce zuciyarsa ya ce. "Shikenan kuma sai yadda hali ya yi wai agola ya saci motar mai gida, wataƙila ma ni da ƙafafu sai dai in gani a jikin mutane, yo wannan matar tun da ta hau kan ƙafafuna, ai na san sai dai a rinƙa saka ni a layin guragu dan na san dai ƙafafuna ba za su amfanu ba sai dai a yanke mini su a bar mini dungulumi" Ya faɗa a ransa yana raya cewa shi bai taɓa haɗuwa da wannan ibtila'in ba. "Mai Gari tashi kar a maimaita yaƙin badar a kan ka" Gwaggo ta faɗa kamar ta rushe da kuka. Ɗif Mai Gari ya yi jin maganar matarsa dan sai lokacin ma ya gane nauyin da yake ji a kan ƙafafun nasa ba shi da wani yawa, wani tsaki ya ja tare da tashi zaune ya wancakalar da Gwaggo daga kan ƙafafunsa ta faɗi gefe guda ya shiga kiciniyar buɗe fuskarsa dan mayafin duk ya tattauye a jikinsa ya kanannaɗe. Ya miƙa hannu ya ɗakko fitila ya kunna haske ya gauraye ɗakin, Gwaggo ya gani ta yi reran tana tana karanto fatiha da salatin annabi dan irin warɓarwar da mijin nata ya mata sai ta ji tamkar wanda aka cillo ta daga saman bishiya yadda ƙashin gwiwar hannunta da kanta a ƙumu a tsakar ɗakin da ko shimfiɗa babu. "Ke dai wallahi Ramma bakya mutuwar tsakar ɗakin ki sai ta wani, dama wannan jikin nawa akwai ya babu kakar wajen uba, da nake lallaɓawa sanadin hawan ƙawarar da shirgegiyar matar can ta mana jiya, shi ne kika zo kika hau kan ƙwabrina da tsakar daren nan sabo da neman sababi dambe da uwar kishiya? Ni ba ma wannan bane abin da ya ɓata mini rai yadda kika saka zuciyata bugun lugude da faɗuwar gaban da na rinƙa yi, da za a yanka jikina ko ɗigon jini ba za a samu ba, sabo da yadda na razana duk tunanina matar nan ce ta ƙara kawo farmaki domin ta saki tusar ta a kan ƙafafuna. Da in banda son a sani gaishe da uwar miji a kasuwa a ce wai tusa wannan idan za a yi ba za a yi ta a sirri ba sai an taho yawon bankaɗa a zaune mutane kamar wasu kiyashi za a sake ta" Mai gari ya shiga faɗa yana surfa masifa amma har lokacin a tsorace yake dan bai gama wartsakewa daga tsoratar da ya yi ba, sai dai duk da haka a hankali yake faɗan dan kar Laila ta jiyo, yo ana tsoronka ɗan mayya, ya ce daga ni har uwata. Gwaggo ko kallon Mai Gari ba ta yi ba hasali ma idanu take wurwurgawa domin ganin in da jaririn yake sai sakin numfarfashi take tamkar wacce ta yi tseran gudu. Dan ko maganar da Mai Garin yake ma ba ta fahimtar komai ita kaɗai ta san abin da take ji. "Wai ba magana ba nake ba kin bar ni sai zuba nake kamar bishiyar kanya to wallahi kar ki ƙara zuwar mini shimfiɗa, tun da dai yanzu kin san ba mu kaɗai bane a ɗakin an kwamustsa mu a ɗaki ɗaya da ƙartan samari" Har lokacin ba ta furta komai ba, zaune ta tashi dakyar tana jin tamkar an an bubbuga mata taɓarya a jikin. Tana tashi ta cigaba da ƙarewa ɗakin kallo amma abin mamaki wai kwalli a ido babu alamar jariri babu dalilinsa. Wasu nannauyin ajiyar zuciya Gwaggo ta sauke ƙwarara a jere guda uku, sannan ta shiga haɗiye yawu muƙut. "Wai haka kawai kin tashe ni daga bacci, kin mayar da ni sauna kira mana shashasha in ka ga sakarai ku taho tare sai wani ciccira idanu kike kamar an kama kwarto a ɗakin sabuwar amaryar data cika sati da tarewa ba, to wallahi idan matar nan ta jiyo hayaniya ta tashi ta zo yin tusa sai dai ta murƙushe ki ke kaɗai" Ya faɗa yana aika mata harara. "Haba kai baka san dalili ne yake sa a leƙa gaban surika ba, in ba akwai abin da ya kawo ni ba mai zai sa in zo wajenka a sulusun daren nan amma ka balbale ni da masifa" "To dama in ba dalili mai sa a leƙa tsiraicin sirika ba, mai zai sa ni faɗuwar gaba ma" "Wannan kuwa amma dai in ba wajenka ba ina zan je tun da kai ne mijina" "Yanzu dai da kika zo a gigicen nan kamar an biyo ki sai wata fisfisga kike kina kalle-kalle kamar a ce kule ki ce cas, mene ne ya tsorata ki" "Mafarki na yi" Ta samu kanta da shirga ƙaryar da ba ta shirya ba. "Mafarki kuma? Yanzu a kan mafarkin ne kika zo kika ɗaga mini hankali kamar dai an aiko ki" "Kai dai bari Mai Gari ai kawai wata tattabara ce na ga tana bina a guje" Gwaggo ta samu kanta da faɗa. "Aikin banza a tattabara mene ne abin tsoro ni na ɗauka ma zaki ne lo kura suka biyo ki, ko baƙin aljani ko dai fatalwa, to sai ki koma ki kwanta dan ni ba zan zauna zaman asara ba in je ban runtsa ba garin Allah ya waye wancan basamudiyar ta hana ni wali" Ya faɗa yana lallaɓawa ya koma ya yi gohonsa tare da rufa da abin rufarsa. "Yo mene ne marabar dambe da faɗa, jaririn da ya fito ta cikin uwarsa ya ƙara komawa yanzu na dawo gida ya zo ya tashe ni tsakiyar dare in masa yankan cibiya in binne uwa, ina lafiya ai sai dai a taya ni da addu'a" Gwaggo ta faɗa a ranta a fili kuma sai ta ce. "Allah sarki ni ma komawar zan yi in kwanta tun da na ga mafarki ne ba a gaske ba" Ta faɗa tana lallaɓawa ta koma ta kwanta a katalalliyar katifar cike da tsoro, baccin da bai ta ƙara komawa ba a kan kunnanta aka kira assalatu sai dai sa'ar ta ɗaya ba ta ƙara ganin jaririn ba. Su Salele kuwa babu wanda ya motsa duk bidirin nan da a ke sai shaƙar baccin su suke. *WASHE GARI* Kowa a tsorace yake da Laila ita kuwa sai ta yi kamar ma ba ta san abin da suke yi ba. Haka ta saka Salele da Taju suka kama manyan ragunan Mai Gari tirkakku har guda biyu aka kai kasuwa aka sayar, buhun shinkafa aka sayo da komai na buƙata da babu a gidan. Gasarar koko ta Gwaggo da take ajiye ta kwano biyu Laila ta saka aka dame kokon a ƙatuwar tukunya na kwano guda aka dama aka karɓi kuɗin suga a gun Mai Gari da yake ƙunshe a ɗaki yana ɗan mammatse hawayen takaicin ragunan da ya ci buri a kan su sai ga shi rana ɗaya wacce ta fi shi ta sayar ta sayi shinkafa, shinkafar ma ƴar gwabnati. Shi ma dama a wajen wasu daga cikin mutanen gari ya yi fin ƙarfi a matsayinsa na Mai Gari ya karɓe, dan shi ko makiyayi ne zai wuce kiwo da dabobin mutane sai ya tsayar da shi ya zaɓi na zaɓa sai dai a faɗawa mai kayan cewar Mai Gari ya ƙwace kuma babu yadda ya iya sai dai ya yi Allah ya isa ba tare da kowa ya ji ba. Biredi manyan sinƙi aka siyo guda goma, lokacin Gwaggo tana ɗana ƙosan kwano ɗaya da rabi. Haka ta gama ta kawo ɗakin da ya zama mallakin Laila ta ajiye a ƙatuwar roba, kokon kuwa a bokitin fanti babba yake, bayan an jere komai Gwaggo ta durƙusa ta ce. "Ranki ya daɗe an kammala" Kallon Gwaggon ta yi a yatsine, ta muskuta dakyar ta tashi ta sakko daga gadon ƙarfen da zuwa yanzu ya lanƙwashe ya wani mogaɗe saboda nauyin da ta masa ga nauyin Nasiru. Tun da ta zauna ta saka kofin silba babba a cikin bokitin kokon ta ciko, ta ajiye ta buɗe birredin ta cira shi a uku duk girmansa ya yi mutum uku su raba su ci su ƙoshi amma ta raba shi gida uku ta kwaso ƙosai ta haɗa da biredin ta ɗauki biredi curi ɗayan da ta raba a uku ta saka ƙosan ta tura shi duka a baki tauna ɗaya biyu sai kawai Gwaggo ta ga ta ɗaga kofin ta kafa kai ta shanye. "Hasbunallahu wa ni'imal wakil" Gwaggo ta faɗa a ranta ganin yadda Laila take cin abincin kamar wanda take zubarwa a ƙasa. Sai da ta ci ta ƙoshi dan kokon ta shanye saura kaɗan ta ɗauki plate ta tsakuri ƙosan ta ɗora biredin guda ɗaya, ta kwalfi koko cikin kofin silba ta miƙa wa Gwaggo ta ce "Ɗauki ga shi nan ki ɓace mini a gani ku je ku raba ku karya" "To, to, to" Ta faɗa tana rawar murya ta ɗauka ta fita a ɗakin. "Haba Ramma ya za ki ɗakko wannan ɗan abincin kamar wanda za a ba wa ɗan kwikuyo (Jaririn kare) Haka kawai kina ganin basamudiyar matar nan tana neman karya mini tattali arziƙi za ta talauta ni, ta nakasta mini dukiya, amma maimakon ki ɗakko abincin a daro yadda za mu ci mu ƙoshi in ɗan hucin takaici shi ne za ki ɗakko abu kamar wanda kika roƙo, ita kuma da babu biyar ɗinta a ciki kika tura mata duka" Mai Gari ya faɗa lokacin da Gwaggo ta shigo ta ajiye abincin da Laila ta basu. "Ni fa ba ni na ɗakko ba ita ta bani kuma wallahi gabaɗaga komai ya zama saura dan ta cinye kuma ina ga ɗanta da yake ta faman bacci ta ajiye wa, kai dai ka ga yadda take haɗiyar abu kamar walƙiya, amma in za ka je ka faɗa mata ta ƙaro mana ga hanya shawara ta ragewa mai rijiya" "In kin ganni a lahira kai ni aka yi" Ya faɗa wasu hawaye suka sirnano masa ya sanya hannu ya goge yana tuna cewa zaluncin da yake yi ne abin ya dawo kansa wato ƙaiƙayi ne ya koma kan masheƙiya. "Haba tsoho ai kawai ka bada kai bori ya hau, dan hausawa sun ce faɗan da ya fi ƙarfinka ka mayar da shi wasa" Salele ya faɗa cikin muryar gagara. "Gaskiya ne Salele ai dama faɗa da mahaukacin kare sai wawa, amma dai na san duniya rawar ƴan mata ce kuma ta fi bagaruwa iya jima" Cewar Mai Gari yana jan hanci. Haka Gwaggo ta kasa kowa ya ɗauka, su duka suna aikawa Taju harara, dan sun san shi ne silar jefa su a masifar da suka tsinci kansu a ciki. Mai Gari lamushewa ya yi ba tare da ya ƙoshi ba sai muzurai yake yana aikawa Gwaggo harara. "Ba ni na kai zomon ba rataya aka bani" Ta faɗa tana taɓe baki. "Oh ni kam sai dai in ce Allah ya mini sakayya, ni da na saba samun malmalar tuwon hatsi in ci in ƙoshi, amma a haɗa ni da ƙwayar ƙosai guda biyar da gutsiren biredi sai wani koko a ƙaramin kofi kamar wanda za a ba ɗan yaye" Ya faɗa yana miƙa ƙafa ya dunguren kofin kokon da ya shanye tsabar haushi. "Ba ni kofina nan kar ka fasa mini ta taƙaice ni ka tashe ni tsaye, ai ni ta mini dai dai wallahi, abin da yau wajen kwanan mu huɗu rabon da a tuƙa tuwon ma a gidan, ga hatsin nan amma ba za a ɗauka ba jiya ma sai wake ka bayar aka yi alala muka ci rana da dare kowa ya kwanta yana sakin iska a ƙarshe ta saka mana ciki muka rinƙa tseran zuwa bayi" Gwaggo ta faɗa tana tashi ta ɗauki kayan ta fita. "Wai Mai Gari ƙoshi ne baka yi ba" Taju ya faɗa yana ƙunshe dariyarsa. "Ubanka ne ban yi ba, na ce ubanka ne ban yi ba" Mai Gari da ya harzuƙa ganin Taju ne ya jaza musu komai ya faɗa kamar ya hau Taju da duka. Shi dai Salele bai ƙara magana ba, dan shi gaba ɗaya bayan rashin ƙoshi ma har da takurar takunkumin da Laila ta saka musu na rashin fita ko nan da can. Tana fitowa ta samu Nasiru ya cinye sauran abincin da Laila ta rage masa sai bokitin kokon hatta ƙosan ko ɗaya babu biredin ma sai ledojin kawai. Mamaki duk ya cika Gwaggo ita dama a tunaninta idan ta zo kwashe kayan ta samu ragowa sai ga shi duk sun cinye. "Kashi zan yi" Gwaggo ta tsinkayi muryar Nasiru yana faɗa wa Laila. "Ramma" Laila ta ƙwala mata kira. "Ni Ramma na gamu da gamona, dama an ce gba da gabanta aljani ya taka wuta" Ta faɗa a zuciyarta ta taho da sauri har tana neman tuntuɓe. "Zai yi kashi ki ɗora shi a fo" "Fo fa Ranki ya daɗe?" Gwaggo ta faɗa tana jimanta al'amarin da ta san dai babu wani fo da zai yi dai dai da mazaunan Nasiru. "Kar ki kai shi ya yi ki zauna neman magana idan ya saki kashin nan a wando kafin ki wanke sai kin yi amai bakwai d... Ai kafin Laila ta ƙarasa Gwaggo ta saɓi Nasiru dakyar ma ta ɗauke shi saboda yadda ya ƙara nauyin caccakar abincin da ya yi, haka suka fito, ta nufi hanyar bayi da shi, ɗaya daga cikin robar wankan su ta ɗakko ta kalli bahon wankan ta kalli mazaunan Nasiru ta jijjiga kai. "Wallahi wannan mazaunan naka masu kama da an hura balan-balan babu inda zai ɗauke su sai dai robar wanka, sai dai a mayar maka da ita fo ɗin kake kashin a ciki tun da duk girman nan da ka yi girman biredi ne ko shadda ba za ka iya hawa ka yi kashi ba" Ta faɗa a ranta tana ɗora shi amma abin takaici da mamaki sai da robar ta tsage daga bakin, saboda bakin robar ma ya masa kaɗan haka ya jibga kashin Gwaggo sai jefar da bahon wankan ta yi dan ba zai amfanu ba. "Haba ni wallahi na gaji ina dalili ina ɗan mafari haka kawai mata ta zo za ta ɓalɓalta mini dukiya, ta karya mini tattalin arziƙi" Mai Gari ya faɗa yana kumfar baki sai wani muzurai yake yana faɗa, a kan Laila ta saka dillalai sun zo sun sayi ɗaga daga cikin gonakansa wanda shi ma asali ba tashi ba ce ƙwata ya yi a matsayinsa na Mai Gari. 'Wannan kuma ai sai ka je ɗakinta ka mata faɗan amma ba wai ka zo kana mini faɗa ba wato ga Ramma kuka mai daɗin hawa" Gwaggo ta faɗa har da gatsinan gefen baki, dan ita cike take da gajiyar girkin jalof ɗin shinkafa da ta ɗora a tukunyar da ake girki da ita a gidan biki. 'Yo ba dole na faɗa ba, tsabar matar nan ta mayar da ni sha ka tafi tirajalin ajansi, a siyar da gonar amma a bani jaka biyu(400) Sai ka ce wanda iyayensa suka ce jeka ka gani" "Kan ka ake ji mahaukaci ya faɗa rijiya, ka je can ka faɗa mata ina laifi dan mai kaza ya tashi da ƙafa, kana gani dai ƙarfi sa yaji rainon yaron nan ya dawo kaina ko ɗazu da ya yi kashi sai jefar da robar na yi, ni ma duk tattalin arziƙin robobina sunan su matattu, haka kawai ba dangin iya ba, ba na baba ba, babu haɗin danga da garahunu ta zo ta addabi mutane" "Ramma" Laila ta ƙwalawa Gwaggo kira. "Allazina iza asabatkum musibatun ƙ...Allazina kafaru wa saddu an sabilillahi..." Gwaggo da ta ringisa har ta fara jin daɗin kwanciyar Laila ta kira ta. Ɗakin ta dosa a tsorace dan gudun abin da zai je ya zo. KAFIN A GAMA FREE PAGES MAI BUƘATA ZAI BIYA KUƊIN KARATU 400 IDAN NA KAMMALA FREE PAGES ZAI KOMA 500 ZA A BIYA TA ASUSUN FAIZA ABUBAKAR 9030283375 OPAY SHAIDAR BIYA TA 09013181851. [8/19, 17:57] Mom mashkur & Afrah: UNGOZOMA (Mai karɓar haihuwa) NA MAMAN AFRAH F.C.W GARGAƊI⚠️ Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ta kowace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowace kafa ba sai da izinina a kiyaye. *PAID ADVERT 1* 💃 Ina mata ƴan ƙwalisa, babbar mace alkyabbar mata, macen mai gyara ita wacce ta isa da miji su o'o sai dai su ga ƙeyar mijinta idan ya wuce amma basu ishe shi kallo ba domin babu abin da za su nuna mata. Gyaran gashi babbar martaba ce da take ɗaga darajar mace, musamman kayan gyaran gashin MAMAN ZEE da ya yi fice a ko ina ake labarinsa. Gani ya kori ji sai an gwada akan san na ƙwarai siyan na gari mayar da kuɗi gida💃💃💃💃💃💃💃💃 Hadaddu Kuma ingantattun kayan gyaran gashin mamanzee(chebe hair set) Wadanda suke dawowa da martabar gashin Kai komai lalacewarsa biiznillahi Rabbi Ga kyau ga inganci ga saukin kudi muddin kika fara amfani da kayammu sekindawo Mana da kyakkyawan labari Kanki zeyi kyau ya rika sheki yayi tsayi yayi laushi duk matsalar da ke cikin kanki zata kau in sha Allah Munada set complete Kuma Muna Bada pieces Haka Kuma Muna Bada Sari Muna turawa akowanne gari kike Kuma Ako wacce kasa kike Phone number *08079130166* *PAID ADVERT 2* 💃 *BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 Page2️⃣3️⃣➡️2️⃣4️⃣ A ɗarare ta shigo ɗakin in da ta samu Laila durƙushe a tsakar ɗaki tana murƙususu tamkar mai naƙuda. "Allah sa ciwon cikin nan ya zama ajalinki kowa ma ya huta yo ina dalili" Cewar Gwaggo a zuciyarta a fili kuma sai ta ƙarasa gaban Laila tana ta faman ambatar mata sannu duk da ba ta san takamaimai abin da yake damunta ba. A take tunnin Nasiru ya ɗarsu a ranta. "Yaro dab kake da zama maraya dan wannan uwar taka tana mutuwa sai dai a nemi gidan marayu a kai ka, dan wallahi riƙon mahaukaci sai sarki, kuma dai ciyar da kai sai ƙaramar hukuma amma mu sai dai ku nakasta mana tattalin arziƙinmu ku haɗa mu ƙaƙƙarfan zumunci da talauci... "Ramma, matso da sauri taki ta same ki wai an haɗa namiji da wankan jego" Maganar Laila ta katse mata zancan zucin da take. "Tawa ta same ni ko taki ta same ki?, ke da za ki mutu ai ke za a faɗawa haka" Gwaggo ta faɗa a ranta tana taɓe baki ta ƙarasa ta tsugunna domin taimakawa Laila, ai durƙuson da Ramma ta yi sai ta ji Laila ta fisgi hannunfa tamkar wacce wutar nepa ta ja, haka Ramma ta ji fisgar da Lailar ta mata kafin ka ce me ye wannan Laila ta ja ƙafar Gwaggo ƙiii sai ga Gwaggo a reran cikin hanzari Laila ta juyo mazaunanta ta zaune Gwaggo. Gwaggo sai ta shiga salati tana ihun neman ɗauki dan tamkar an loda mata buhun siminta goma haka ta ji nauyi jiƙit Lailar ta mata. "Wayyo Allah na, abin na ba a ne an ce da kare mai sunan mata" Gwaggo ta faɗa a ranta tana ganin yadda gaba ɗaya mazaunan Laila suka mata rumfa ba ta ganin komai sai Lailar a samanta. Tun da Laila ta zaune Gwaggo take sakin iska kamar an cakawa tayar mota ƙarfe sai sacewa take babu birki Gwaggo sai addu'a take saki a zuciyarta ga wari ga kuma nauyin Laila. Can Gwaggo da ta ga abin ba na ƙare bane Laila ta ƙi ɗaga ta sai kawai ta fara zubar hawaye a take tunnin su Mai Gari ya faɗo mata, na jiya da suke ba ta labarin yadda Lailar ta zaune su ta rinƙa sakin tusar a kan su tamkar wanda aka aiko ta, har ma Mai Gari yana cewa ko dai kansa ya logaɓe tana ganin jiya da goho ta kwanta saboda ciwon da fuskarsa da kansa suke masa amma lokacin da suke labarta mata, amma ta mayar da abin labarin ƙanzon kurege wato ba komai ba dan tana tunanin raki ne kawai irin nasu da rashin juriya, sai ga shi ita cikin mintuna ƙalilan tana neman ɗauki bata ma san su Mai Gari su iya mintunan da Lailar ta kwashe jibge a kan su ba. Cikin dibara ta ɗago bakinta duk da tana jin warin amma a haka ta jure dan idan ka ji ana ba zan iya ba to bai kama ka bane. Bakinta ta hangame ta saiti ɓari ɗaya na mazaunan Laila ta ɗora mata haƙoranta talatin da biyu. Laila da hankalinta kwance take sakin tusa babu ko ƙaƙƙautawa sai wani rausaya kai take kamar ƙadangaruwa ɗ, har wani lumshe idanu take kamar ɗan mayen da ya sha ya bugu dan ita a wurinta yin tusa ba ƙaramar samun lafiya bane a gare ta. Tana cikin wannan yanayi na jin daɗin fitar da iskar sai kawai ta ji saukar cizo a mazaunan ta, yadda Gwaggo ta saka tsokar mazaunan Laila a tsakanin haƙoranta na sama da ƙasa ta dantse tamkar kaca a jikin keke ko sakawa ba ta yi ba. A kiɗime Laila ta yi hanzarin tashi dan sai ta ji tamkar an caka mata tsinin mashi sai dai tana tashi sai ta ji gefen mazaunan nata in da Gwaggon ta damƙa da haƙori gaba ɗaya a riƙe yake, tamkar an saka mayen ƙarfe a jikin ƙarfe, ja take amma ina Gwaggo ta riƙe wurin gamgam dan har idanu ta rintse ta dage ƙarfinta dan so take sai Laila ta gane shayi ruwa ne, dan ta lura a zaman nan da ta fara daga jiya zuwa yau idan har ba sa yunƙurin ƙwatawa kansu ƴanci to tabbas bayan dara akwai wata caca. Dan ta fahimci duk abin da suke yi ihu ne bayan hari. Laila tsabar azaba da sauri ta sake komawa ta zaune kan Gwaggo da bakinta yake a sama, ƙara kaimi Gwaggon ta yi wajen datsa haƙoran Laila ta sake tashi tana faɗin. "Ramma ki yi wa Allah da ma'aiki kar ki tsunguye mini tsokar ɓarin mazaunai" "In dai da hankalinki nan gaba ko an ce zaune Ramma ba za ki fara ba ma" Gwaggo ta faɗa a ranta cike da mugunta duk da a wani ɓari na zuciyarta tana shakkar abin da zai je ya zo na hukunci da Lailar za ta mata sai dai ta san ko ma mene ne sai dai ta mata horo da wani abun amma ba wannan ba dan ta riga da ta san hukunci da zaunewa dole ya zama tarihi, dan ta tabbatar mazaunan Lailar sun cizu. Laila jin abin ba na ƙare bane wai tsoho ya samu amarya budurwa sai kawai ta shiga tafiya domin ko ta samu Gwaggo ta saka mata mazaunan haka ta fara tafiya ƙafafu a tattale kamar sabuwar ƴar maye ga shi ta ɗan ranƙafa kamar wata tsohuwa. Ƙiiii take jan Gwaggo da take kwance reran a ƙasa haka suka shiga zagaye ɗakin amma Gwaggo dan ƙarfin hali ɓarawo da sallama ba ta saki Laila ba, wani marayan kuka ne ya ƙwacewa Laila dan dafin haƙorin Gwaggo ya wuce tunaninta. Gwaggo jin Laila ta fara kuka sai haka ya nuna mata cewa haƙarta ta cimma ruwa dan haka sai ta saka cizon da ta yi wa Lailar, cikin tafiya ƙafa a gwale tana sakin numfashin wahala ga hawaye yana kwaranya sai ta lallaɓa ta je jikin gadon ɗakin ta daddafe da hanayenta ta saki wani nishi da ƙarfinta tamkar mai naƙudar da ɗa yake shirin fitowa daga jikinta, a take wata tusa mai ƙata booooot ta fito a jere har guda huɗu, karkata kai Laila ta yi gefe ta ɗora kan nata a kan kafaɗarta tana sauke numfashin wahala. "Wa ya faɗa miki barno gabas take, dama ai ni na san salon munafurci ne wai auren mijin ƙawa, har za ki ce bakya yin tusa sai kin zauna a kan mutane, yanzu kuma da kika ji uwar bari a kan uban wa kika saki tusar? Duk da na san ramako zai biyo baya wai auren uban ƙawa, amma dai ai yanzu na san na yi wai makaho ta taka kashi ko ma mai za ki mini na san sagegeduwa ne bin diddigin budurwar miji" Gwaggo da take yashe reran a tsakar ɗakin ta faɗa a zuciyarta tana kallon Laila da take tsaye har lokacin tana yadda take. "Ramma ni kika yi wa wannan ɗiban albarkar? To ki kwana da sanin bashi kika ci kuma sai na rama wai miji ya yi wa matarsa kishiya ta auri ubansa bayan ta bar gidan" Laila ta faɗa a zuciyarta tana jin haushin abin da Gwaggon ta mata dan ta san yanzu tusar nan da ta saki ba a kan kowa ba to tabbas sai jikin mazaunanta sun tsage. "Sannu Ranki ya daɗe, sannu da dole ke dai kam kin haɗu da jarabawar rayuwa mai wahala tusa a ce mutum ya yi ta sakin tusa kamar bodari" Cewar Gwaggo da ta yi wani firgigit ta tashi zaune tana murza idanu ita ala dole yanzu ta farfaɗo. Banza Laila ta mata tana juyowa ta shiga aika mata da harara har lokacin Gwaggon tana murza idanu har wani gwale su take. "Ai mun samu lafiya tun da na samo maganinki" Gwaggo ta faɗa a ranta tana danne dariyarta dan ita jin daɗi ji take tamkar ta tashi ta shiga taka rawa. "Ni kaina ban san halin da nake ba, tun da kika zaune ni sai na rasa suma na yi ne ko kuwa tsofaffin aljannun kaina ne da suka daɗe basu tashi ba suka tashi, dan har wani abu na ji an hangame bakina ana saka mini kamar wasu ƙarafa Allah dai ya sa basu cake ki ba" Gwaggo ta faɗa cikin sanyin murya har da wani rausaya kai ita ala dole tana so ta nunawa Laila cewar duk abin da ya faru ba ta san ya faru ba dan ba ma a cikin hayyacinta take ba. Wani kallo kawai Laila ta mata na kin ma ranawa kan ki hankali ta ɗauke kai kamar ma ba da ita Gwaggon take ba. "Taɓ ba dai baki yarda da ƙaryar da na shirgo miki ba lallai akwai badaƙala wai dambe da sirika a titi" Gwaggo ta faɗa a ranta tana haɗiye wani yawu muƙut dan ta san tabbas dai bayan dara akwai wata caca. "Za ki san ni kika yi wa haka dan sai kin gwammace kiɗa da karatu, domin tsakanina da ke akwai ƙura wai mai kaya ya kama ɓarawo da kayansa, dan sai in da mai ya ƙare shiga motar mahaukaci" Laila ta faɗa a ranta tana ɗan jijjiga kai a fili kuma sai ta ce. "Ayya! Ai ni ma na lura da haka babu komai ai dama mutane masu shafar aljannu sun saba yin haka" "Tabbas kin yi kuskure da kika yarda da maganata dan na samo lagwanki mu zuba ni da ke, dan yarda da maganata da kika yi haƙiƙa kin yi ƙundunbala wai naushin mashayin giya" Gwaggo ta faɗa a zuciyarta a fili kuma sai ta ce. "Yawwa godiya nake Ranki ya daɗe" "Za ki iya tafiya" Cewar Laila cikin murtuke fuska dan ta san yanzu sai ta yi jinyar mazaunanta, saboda tsagewar da suka yi dan ta san duk lokacin da ta yi tusa ba a kan mutum ba to tabbas sai ta samu wannan matsalar. Dakyar Gwaggo ta muskuta ta tashi tsaye tana jin jikinta tamkar wanda ƙattan maza suka yi wa dukan kawo wuƙa saboda ciwon da jikinta yake musamman da Lailar ta tashi daga kanta ta sake komawa ta jaɓe kamar kayan wanki duk a kan nata ga bakinta har wani zafi yake saboda ciwon da ta daddage ta yi, amma dai da dama-dama wai kibiya a ido tun da ga shi yanzu kwalliya ta biya kuɗin sabulu. Haka ta taso ta fito daga ɗakin ranta fari ƙal, tana shiga ɗakin nasu ta zauna tana ta tiƙar dariyar ƙetar da ta yi wa Laila, shi kuwa Mai Gari sai taya ta dariyar yake yana faɗin ta masa dai dai duk abin da suke yi basu san Laila tana tsaye a laɓe tana jin duk abin da suke cewa. Haka dai aka yi wunin ranar kowa ya sha jinin jikinsa Laila kuma zaman kirki ma ba ta iyawa saboda yadda mazaunanta suke mata raɗaɗi. Gwaggo kuwa abincin ranar da ta dafa jikinta sai ciwo yake dan ba laifi ta aikatu. *DARE* Zaune suke a ɗakin su duka kowa da abin da yake tunani, Mai Gari ya rasa mai yake masa daɗi dan ya saba ya ci ya ƙoshi amma wunin ranar yau duk sai sam barka domin abincin da ya ci a yau akwai ya babu ne kakar wajen uba, dan haka yanzu cikinsa sai kiran ciroma yake kawai baccin ma ya gagare shi shi ne ya tashi zaune ya jingina da bango yake faman ambaton Allah ko ya samu sassaucin yunwar da yake. "Bunnu ta ƙi binnuwa" Salele ya faɗa cike da sheƙiyanci. "Inuwa" Taju ya ba shi amsa yana danne dariyarsa dan ya san Mai Gari Salele zai yi wa sheƙiyanci shi ya sa ya fara haka. "Na waiga -na waiga ban ganta ba" "Ƙeya" Taju ya ƙara ba Salele amsa. "Shanun gidanmu dubu-dubu amma a turke ɗaya ake ɗaure su" "Tsintsiya" "Faɗe yaro faɗe babba" Salele ya faɗa lokacin gaba ɗaya dariyar da yake dannewa ta fara bayyana a cikin maganarsa. "Yunwa" Taju ya faɗa yana tuntsurewa da dariya, dan dama ya san kwanan zancen dan Salele ya san Mai Gari yana jin yunwa shi ya sa ya tarki zayyanowa dan ya zo in da zai ce faɗe yaro faɗe babba. Salele ma dariyar yake yi har da ƙyaƙyatawa dan kana kallon idanun Mai Gari za ka san ya haɗu da gamonsa wato yunwa. "Allah dai ya tsinewa yunwar, sakarkarun banza sakarkarun wofi, ban da iya shege taɗe ƙafar makaho ni za ku zauna kuna yi wa sheƙiyanci wancan ba Kakar ku bace ko ita yunwar ba ta faɗe ta ba sai ni marenin wayon ku" Mai Gari da dama kaar jira yake ya fara surfa faɗa yana kumfar baki tamkar dai su ne suka hana shi abinci ya ci ya ƙoshi. "Ran Mai Gari ya daɗe Allah dai ya taimaki Mai Garin Gumurzu wa ya isa ya ja da kai" Salele ya faɗa. "Sai yunwa" Taju ya faɗa har lokacin yana dariyar, dan ya kasa riƙe dariyar musamman yadda Mai Gari yake nuna su da yatsa tamkar wanda suka yi masa sata. "Wallahi Taju ka kiyaye ni, mutumin banza da wofi ni nan da kake gani labule ne ni rufin asirin ɗaki, kuma kowa ya ci tuwo da ni miya ya sha, hatsabibin banza in banda kai sha ka tafi ne kana soja amma ka kawo mana jaraba gida ai ni gwara da ka cire kayan sojojin ka ajiye ni ban ga amfaninsu ba aikin banza harara a duhu" Ya faɗa yana jan tsaki tare da komawa ya jingina da bango jin idanunsa suna ganin duhu-duhu saboda yunwar da yake ji. "To Mai Gari ya kake so na mata ne ka dai ga yadda take ƙatuwa" "Yo ƙatuwar me, girman banza ne fa yanzu wannan soson katifa sai ya fi ta nauyi abu shirgaga kamar bijimin sa... "Ramma, Ramma" Muryar Laila da ta turo ƙofar ɗakin da take kira Gwaggo ta katse wa Mai Gari maganar. Gwaggo da take ringishe abin duniya ya haɗe mata goma da ashirin tana tsoron bacci ya ɗauke ta dare ya tsala jaririn jiya ya zo mata sannan a gefe ɗaya tana fargabar zuwa kiranta UNGOZOMANCI dan ita gaba ɗaya yanzu abin ya fice mata a rai. "Laila, Laila, Laila, sarauniyar kyau Laila, mai halin dattako, tausayi da kyautatawa riƙon amana Laila" Mai Gari da ya fara waƙar da babu shiri tamkar sabon maroƙi, shi kansa jin baitocin ya yi suna masa dirar mikiya bai ma san asalin waƙar ta ya aka yi ta zo a kansa ba. Burinsa bai wuce a ce Laila ba ta ji abin da ya faɗa ba dan ya san in har ta ji to kashinsa ya bushe. Ko kallonsa Laila ba ta yi ba duk irin yaƙi da ƙugin da cikinsa yake masa da ya yi, ya hangame baki yana rattabo baitikan. Gwaggo kuwa gabanta ne ya bada rasss, dan babu abin da ta ƙi jini irin a zo kiranta karɓar haihuwa dan yanzu har ta fi ƙin jin tsoron kiran Laila ta tsani kiran karɓar haihuwar tun da ta samu tangarɗar nan. "Na'am Ranki ya daɗe" Ta faɗa lokacin da ta tashi zaune tana gyara ɗaurin ɗankwalinta da ya sunce "Duk kun cikawa mutane kunne da hayaniya, ana ta buga gida bakwa ji" "Bugun gida kuma Ranki ya daɗe?" Gwaggo ta yi saurin tambaya gabanta yana faɗuwa tana fatan Allah ya sa ba ita aka zo kira ba. "Wasu ne suka zo kiranki, tun da ke kin san sana'arki kamar fashi da makami take, wato har da dare ma ana zuwa kiranki ai ba kwa kw surutu ba yanzu sai ni na je na tambayo da bugun ƙofar ya dame ni" "Allah ƙadiran wa maridan wa aliman wa hayyan" Gwaggo ta faɗa a ranta tana jin kamar dai ta suma saboda tsoro da tashin hankalin da ta shiga, dan ita ba dan mutanen gari za su ce ta gaza ba da ta daina karɓar haihuwar sai dai ta riga da ta san cewa kasawa ce yin hakan kuma ma alƙawarin Kakanta da ya bar mata sana'ar nan ya mata hanyar samunta. "Wallahi ka bar mini gadon wahala" Ta faɗa a ranta tana jin ƙwalla tana ciko mata. "Wai ya ana miki magana kin tsaya wani abu" Laila ta faɗa a zafafe wanda hakan ya sanya Mai Gari babu shiri ya tashi tsaye dan shi kansa bai san ya aka yi ya tashi ba ya dai gan shi a tsaye yana dawurwurin nema in da zai bi, saboda a tsorace yake matuƙa ya san matsawar dai Lailar ta ji abin da yake faɗa a kan ta na wulaƙanci to tabbas za a kwashi ƴan kallo. Gwaggo kuwa cikin sanyin jiki ta tashi ta ɗakko aska da zaren ta fara tafiya tamkar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki dan ko jiya da ta fita aikin INGOZOMANCIN nan gidan Malam Mammani haka ta je ta sha baƙar wahala ta dawo babu ko sisi yo wa yake ta kuɗi ma yana ta ceton rai da ta samu ta kuɓuto dakyar. Juyawa Laila ta yi ta fita Gwaggo ta take mata baya, Mai Gari kuwa da sauri ya koma ya zauna yana maida numfashi ganin Laila ba ta ji abin da yake cewa ba dan ya san da a ce ta ji to tabbas da ta yi magana. Salele da Taju kuwa dariyar da suke dannewa ce ta fito fili dan tun shigowar Laila suka yi wa idanunsu masauki a kan Mai Gari yadda ya yi wani wurjanjan kamar kwarton da mai gida ya kama. "Ansitu lilƙaniyatukum" Mai Gari ya faɗa. "To fa Mai Gari ya fara koyo larabci wato mu yi shiru dan ƙaniyar mu" Taju ya faɗa yana ƙara dariya har da riƙe ciki. Salele ma dariyar yake yana rufe bakinsa da tafin hannunsa. "Ku ungo ku raba" Mai Gari ya faɗa yana watsa musu yatsun sa biyar alamar daƙuwa. *KAFIN A GAMA FREE PAGES MAI BUƘATA ZAI BIYA KUƊIN KARATU 400 IDAN NA KAMMALA FREE PAGES ZAI KOMA 500 ZA A BIYA TA ASUSUN FAIZA ABUBAKAR 9030283375 OPAY SHAIDAR BIYA TA 09013181851* . [8/19, 17:57] Mom mashkur & Afrah: UNGOZOMA (Mai karɓar haihuwa) NA MAMAN AFRAH F.C.W GARGAƊI⚠️ Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ta kowace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowace kafa ba sai da izinina a kiyaye. *PAID ADVERT 1* 💃 Ina mata ƴan ƙwalisa, babbar mace alkyabbar mata, macen mai gyara ita wacce ta isa da miji su o'o sai dai su ga ƙeyar mijinta idan ya wuce amma basu ishe shi kallo ba domin babu abin da za su nuna mata. Gyaran gashi babbar martaba ce da take ɗaga darajar mace, musamman kayan gyaran gashin MAMAN ZEE da ya yi fice a ko ina ake labarinsa. Gani ya kori ji sai an gwada akan san na ƙwarai siyan na gari mayar da kuɗi gida💃💃💃💃💃💃💃💃 Hadaddu Kuma ingantattun kayan gyaran gashin mamanzee(chebe hair set) Wadanda suke dawowa da martabar gashin Kai komai lalacewarsa biiznillahi Rabbi Ga kyau ga inganci ga saukin kudi muddin kika fara amfani da kayammu sekindawo Mana da kyakkyawan labari Kanki zeyi kyau ya rika sheki yayi tsayi yayi laushi duk matsalar da ke cikin kanki zata kau in sha Allah Munada set complete Kuma Muna Bada pieces Haka Kuma Muna Bada Sari Muna turawa akowanne gari kike Kuma Ako wacce kasa kike Phone number *08079130166* *PAID ADVERT 2* 💃 *BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 Page2️⃣5️⃣➡️2️⃣6️⃣ Gwaggo tana buɗe gida ta ga mai unguwar gabas Malam Lawandi, shi da babban ɗansa Audu matashin saurayi ne. "Ina wuni Malam Lawandi" Gwaggo ta faɗa tana muzurai ita ba dan ba dan ba da ta daina INGOZOMANCIN nan dan dai kawai babu yadda za ta yi ne. "Haba Ramma ai gaisuwa ma ƴar ta yi daɗi ce Zuwai da Talatu suna can hajaran majaran kamar ba sa yi ba naƙuda kowacce haihuwa ta zo gadan-gadan amma ke kina ta gaisuwa" Ya faɗa a ruɗe dan shi gaba ɗaya hankalinsa a tashe yake, shi kuma Audu ɗansa sai muzurai yake alamar daga bacci aka taso shi ba da son ransa ba. Gwaggo tana shirin yin magana Laila ta zo ta banko ƙofar gidan baram har ta kusa bige Gwaggon da take tsaye a kusa da jikin ƙofar ta matsa gefe da sauri ganin za a haɗa da hannunta, dariyar yaƙe kawai ta yi tana faɗin. "Allah sarki to babu damuwa ai sai mu ɗunguma zuwa gidan naka, ashe su duka biyun ne ma suke naƙudar ai da na ga ita Zuwai cikin nata ya fi yin tirtsitsi zatona sai ta rigayi Talatu" Ta faɗa lokacin da Malam mai unguwar gabas ya shiga gaba ita da ɗan nasa Audu suka take masa baya. "Ni Ramma ina ganin abin al'ajabi wai ango ya kwana da ƙunzugu, shikenan ni haka zan ke rayuwa kullum daga wannan sai wancan duk dare kowa yana can yana bacci amma ni in ƙare a gantale ina wa mata INGOZOMANCI ta faɗa a zuciyarta tana sakin wata ƙatuwar hamma ta rashin bacci da kuma guntuwar yunwar da take addabar ƴaƴan hanjinta. "Ku dakata da tafiya zan baku tsaraba" Wata murya daga saman bishiyar kuka da take gefen hanya ta faɗa lokacin da suka zo setin ta. A sukwane Gwaggo ta yi taku ɗaya biyu sai ga ta sun jera da Malam Lawandi, su duka suka cure a wuri guda dan babu halin gudu, ba ta yi wata-wata ba ta ɗaga babbar rigarsa da take jikinsa ta shige sai ga kanta ya fito daga hannun babbar rigar. Audu ma ganin haka sai ya shige cikin rigar Malam ɗin daga ɗaya gefen da yake ita Gwaggo ta gefen hannun hagu ta shiga, shi kuma sai ya shiga ta gefen hannun dama, sai ya zamana kan Malam Lawandi ne a tsakiya su kuma nasu yana gefe da gefe. "Ku ungo tsarabar tsamiya a yi wa masu jego kunu, ga kanwa kuma in za a dama musu kunun kanwa" Aka sake faɗa daga saman bishiyar. "Matan Baba ne dama masu naƙudar shi ya kamata ya karɓa musu tsarabar" Audu ya faɗa yana rarraba idanu. "Wannan yaro da kaifin basira kake ni ma bani da haɗi da masu haihuwar INGOZOMANCI kawai zan je tun da ai ba laifi bane, duk cikin taimako ne gani na yi abin duniya mene ne ? Kaza ta jawo muzuru kwanan gida"Gwaggo ta faɗa tana kallon Audu muryarta har karkarwa take. "Shikenan yau kashina ya bushe na yi angamo da fatalwar nan da ake ta labari" Malam Lawandi ya faɗa a ransa yana jin kamar ya kurma ihu. "Malam ko in sakko in kawo maka" Aka faɗa dai daga saman bishiyar. "To fa abin na yi ne an biyawa bazawara aikin hajji" Gwaggo ta faɗa a ranta tana jinjina maganar. "Dan Allah ka mini rai, wallahi in haihuwar ce ma bakwa so a yi ina zuwa gidan sai kowacce a ce ta rufe mafitar ɗan nata (HQ) Da ɗan diras(Pant) su daina naƙudar, ko kuma a ɗinke musu wurin haihuwar shikenan ba sai sun haihu ba, amma ni ina zan kai tsamiya da kanwa a talatainin daren nan" Malam ya faɗa yana jan hanci dan ya ɗan kalli fatalwar saman bishiyar farin kaya ne a jikinta sai wata baƙar leda da take miƙowa. "Haba kai kuwa ka karɓa mana so kake sai ya sakko kai da ka samu tsuntsu daga sama gashashshe? An hutashsheka da siya In ba abin rabo bane tsintar ƙwan jaki ta yaya haka za ta faru" Gwaggo ta faɗa tana fatan Malam Lawandi ya karɓo ledar kar abin ya shafe su gaba ɗaya. "Ke kuwa Ramma ki karɓarwa ƴan uwanki mata saƙon nan mana, kin ga ai abin babbane INGOZOMA da adda" "Eh Gwaggo Ramma" Audu ya faɗa dan shi zuwa lokacin fitsari ya fara sirnano masa saboda tsurewar da ya yi. "Baba dan Allah ka karɓi tsamiyar nan da kanwa kar fatalwar nan ta sakko kusa da mu" Audu ya faɗa cikin raɗa-raɗa "Babu abin da zai sa in karɓi abu a hannun fatalwa, kai ba ɗana bane ka wakilce ni mana" "Baba kai fa ka sha miya ni kuwa yanzu nake ganiyar shekaruna" "To dan ubanka ba miya ba ko kukar kaɗi zalla na haɗiya ba zan karɓa ba, kai ko ma baishire kukar kanta na cinye ba zan karɓa ba, kuma an ce maka duk tsufan mutum yana son mutuwa ne" Shi ma ya faɗa duk cikin raɗa. Gwaggo kuwa idanunta a kafe a bishiyar nan ganin fatalwar ta fara tasowa daga saman bishiyar a saman iska. "Ƙalu innnalillahi wa inna ilaihir raji'un abin sai ido bebiya ta auri makaɗi, amma dai Malam Lawandi da ka sako ni a wannan matsala ka takaice ni kuma ban yafe muku ba an ce da karuwa hayo gado, dama ni ma ganganci ne haihuwa damuna" Gwaggo ta faɗa a zuciyarta. Gwaggo da Audu ganin fatalwar tana neman sakkowa da sauri suka ƙanƙame Malam Lawandi da ya buɗe baki yawu yana kwaranya shi bai ma san ma'anar buɗe bakin yawu yake zuba ba shi dai ya tsinci kansa ne da aikata haka. "Allah ka yafe mini na rungumi mijin da ba nawa ba, wuya in ji tsula wallahi ba dan ana yanayin tsoro ba ba zan iya rungume mijin Zuwai da Talatu ba suna can a halin rayuwa ko mutuwa suna naƙuda a ce ni ina maƙure da jikin mijin su kamar wata kyanwa abin na dubawa ne" Cewar Gwaggo a zuciyarta. Gwaggo ganin abin ya sakko ƙasa sai dai ba wai ya dira a ƙasa bane kawai dai a saman iska yake, cikin rigar Malam ta ƙara shigewa har ta yi nasarar saka kan nata a wuyan rigar Malam Lawandi in da kansa yake sai ya zamana kawunan su ne su biyu a cikin wuyan rigar. Audu ma ganin za a yi babu shi sai ya turbutsa nasa kan shi ma Mai unguwa faɗi yake. "Audu rigata ce fa ta ƙaramar sallah, ko baka gane shaddar ba, yau ma ɗaurin aure na je da ita da na dawo na rataye shi ne kiran nan, na gaggawa da aka mini na naƙudar su Zuwai na sako ta na taho dan Allah kar ka mini sanadiyyarta" Ya faɗa jin Audu yana tutsa kansa, ɓeeet ƙaran yavewar rigar Mai unguwa ta ziyarci kunnuwansa wanda sai a lokacin ne ma ya lura da kan Gwaggo duk a cikin wuyan rigar tashi. "Oh Allah na shiga uku ni Lawandi Allah ka kawo mini agaji, ashe shi ya sa nake jin wuyan rigar ta matse ni, ashe har da kan matar Mai Gari a cikin wuyan rigar, shikenan sun nakasta mini rigar shaddata ta ƙaramar sallah shaddar shiga taro" Ya faɗa a ransa yana jin kamar ya yi kuka, musamman idan ya kalle su ta wutsiyar idanunsa ya ga kan nasu a ciki sai ciccira idanu suke musamman Audu. Su duka ukun sai a lokacin suka lura da kan fatalwar da yake gabansu na ƙwarangwal ne ba na mutum ba. A take Audu ya saka hannunsa na dama yana shafo hawayen da suka ɓalle masa tamkar an buɗe famfo sai kuma ya saka hannunsa na dama ya tara tafin hannun ya tara ruwan hawayen a cikin hannun, da shi kansa bai san dailin yin hakan ba tsabar tsoron da ya shiga ne. Malam Lawandi hannu biyu ya saka yana ta shafar kai tamkar mai alwala, haka yake shafar kan tun daga gaban goshin har sai ya kai ƙeya sai ya sake dawowa, sai kuma ya yi shaƙar hanci ya face ya sake yin wata shafar kan ya yi hakan ya maimaita sama da sau goma, kawai sai yi yake kamar wanda aka ba umarnin yin hakan. Gwaggo Ramma tun da ta yi ido biyu da kan ƙwarangwal ta runtse ido ta buɗe ta tabbatar da ƙwarangwal ne ramin idanun ma babu komai a ciki a take ta buɗe idanun tare da sako hannunta, ita ma ta zame kan hijabinta ya dawo wuyanta babu shiri ta cire ɗankwalinta ta jefar ba ta ma san inda ya faɗa ba kitso kawai ta fara yi wa kanta da kanta sai ta kai rabin kitson sai kuma ta saka yatsunta ta tuje kitson, da yake dama ba wani kamuwa yake yi ba tsabar tsoro da fargaba ne ya sa ta rasa mai ma za ta yi. Wuyan rigar Malam Lawandi kuwa ya yage gaba ɗaya dan yanzu har wajen kafaɗarsu wuyan rigar ya je. A hankali fatalwar ta ƙara matsowa gaban su, wanda hakan ya hassada su duka ukun suka ji saukar fitsari ba tare da burki ba, daga saitin Gwaggo ta tsaya har lokacin a kan iska take ƙafafunta a naɗe tamkar wacce take a zaune Gwaggo da numfashinta ma ya tsaya cak ganin ga ta ga fatalwa sai ta ji fatalwar ta kai hannu kan gashin kan nata ta ce "Bari na miki kitson ko" "Yau na ga abu banbarakwai wai namiji da suna Hajara, in ba dan fallasa auren bashi ba, ni cewa na yi ki mini kitso ki bar ni mana in yi da kaina, ai guntun gatarinka ya fi sari ka bani, duk da dai na san idan makaho ya ce a yi wasan jifa to ya taka dutsi ne amma dai kai ka faɗa? Uwar sarki a doki ai kura ma ta san gidan mai babbar sanda sai dai kamar da gaske wai karuwa ta ga noman ɗan koli" Gwaggo ta faɗa a ranta jikinta yana karkarwa jin hannun fatalwar ya taɓa gashin kanta, da alama dai da gaske fatalwar kitson za ta mata. "Wa ƙulna ya naru kuni bardan wa salaman ala ibarahim" Gwaggo ta daddage ƙarfinta ta faɗi addu'ar da ake tofawa mutum a wajen ƙuna idan ya ƙone ita kanta dakyar ta yi yaƙi da baki da ƙwaƙwalwarta ta samu furta lafazin, duk da muryarta tana rawa har da disko ma. Fisgar gashin fatalwar ta yi da ƙarfi sai kuma ta sake shi yadda Gwaggo za ta ji a jikinta. "Wayyo ni a garin nana wayyo ni, ni dodo na yi ya kai autan iya da baba har na fi" Gwaggo ta ƙara samun nasarar karanto wata waƙa daga cikin tatsuniya da ake yi wa yara, yadda jikinta yake karkarwa za ka ɗauka a cikin frezer aka saka ta ta ɗau mugun sanyi amma ba komai bane sai tsoron da take ciki. Suuuu fatalwar ta tafi a kan iska ta tsaya a daidai kan Malam Lawandi da har lokacin yana ta shafar kai da shaƙar hanci ganin layi ya zo kansa bai san lokacin da ya ƙara ƙaimi wajen shafar kai da shaƙar hancin ba, ganin tana dab da shi sai ma ya ƙara haɗa wa da ƙwaƙwalar kunne. "Ai sai an yi shaƙar hanci ake wanke fuska sai kuma a wanke hannu sannan a yi shafar kai sai kuma ƙwaƙwalar kunne ya biyo baya" "Allah bada lada!" "Bari ka gani" Cewar fatalwar tana miƙa hannun ta da Malam Lawandi ya ji kamar wani ƙarfe sai uban farata zaƙo-zaƙo, ta shiga shafa masa fuskarsa tamkar dai tana masa wankin fuska. "Iza waƙa'atil waƙi'eh, laisa li waƙa'atiha kazibe, kafidatur rafi'eh, iza rujjatur ardu rujje" Malam Lawandi ya shiga karanto suratul waƙi'a cikin kira'ar warshu yana karatun yana kuka. Kuka yake hawaye yana zuba kamar an buɗe bakin famfo ga shi har lokacin suna kaɓace a cikin babbar rigarsa su duka ukun Audu jin mahaifinsa yana karatu yana kuka sai shi ma ya shiga rusa nashi kukan, saboda an ce wai yi wa kanka hisabi kafin a yi maka, domin shi bai iya karatu ba sai shegen yawo sai gagara ya sa a gaba yau ga ranar addu'a da karatun alƙur'ani to shi da bai iya ba. "Yau ni Audu, Aududu ɗan Malam na ga ta kaina, ga shi zan ga abin da ya turewa buzu naɗi, na yi saki na dafe wai mace ta rabu da mai kuɗi ta auri talaka, ga shi na ga fatalwar nan ta sako mu a gaba sai in da mai ya ƙare shiga motar mai taɓi" Ya faɗa yana rushewa da kuka tare da cigaba da tara hawayen nasa kamar yadda yake yi, dan ya fara sarewa tun da ya ga mahaifinsa ma da ya iya karatu ga shi yana yi yana kuka yana ganin kamar ma dakyar ya warto karatun saboda ruɗu bare kuma shi da cikakkiyar fatiha ma bai iya ba gwara ma wasu abin sai dai in ji ya yi ana faɗa. Gefen Audu ta matsa ta tsaya ta ƙura masa idanunta da babu ƙwayar idanu a ciki abin da ya ƙara ruɗa masa ciki kenan har yana jin tamkar zai fara gudawa, dan zuwa lokacin ya ji fitsarin nasa ya ɗan ƙafe da alama ya ƙarar da fitsarin marar ta shi. "Bari a tare maka haway... Tun kan ta ƙarasa faɗa Audu ya ce "Na hutar da ke dan Allah ki mini rai" "Haba ɗan samari kyakkyawa ai aiki bai kamaceka ba" Ta faɗa tana kai hannu ta shafo fuskar Audu. "Baba dan Allah ka bani addu'a ko ta korar sheɗanun mutane ce ba sai ta sheɗanun aljannu ba, ni ko addu'ar saka tufafi ce ma ka bani, dan Allah Babana Allah dai ya maka albarka, Baba ka bani addu'ar shiga kabari in za a saka ni a ciki in yi dan kar in yi fatalwa in ke tsorata mutane in na mutu" Audu yake ta faɗa a gigice dan duk ya fita a hayyacinsa saboda tsabar tsoro. "Wa alfaya sayyidaha ladal baab, ƙalu ma jaza'u man arada bi ahalika su'an illa an yusjana au azabun aliim" Malam Lawandi da ba ya ma fahimtar maganar ɗan nasa Audu yake janyo ayar da bai fara daga farkonta ba, shi kansa da za a saka masa wuƙa a wuya bai ma san a wace sura take ba ya sai ji ta zo masa a bakinsa ne. "Ba zan iya ba Baba, ya kake faɗa mini karatun kamar kana mini ɗori, kai da za kake faɗa da ɗaɗɗaya da ɗaɗɗaya amma ka kamo aya mai wahalar faɗa dan Allah ka faɗo mai saukin faɗa ko ni ma na kuɓuta" Ya faɗa yana kuka yana karkarwa dan har lokacin hannun fatalwar yana kan fuskarsa tana share masa hawayen. "Ma agne anhu maluhu mawakasab, sayyasla naran za ta lahab, wa mar'atuhu hammalatal haɗab" Malam Lawandi ya cigaba da karanto duk ayar da ta zo bakinsa. "Zan bige kar ka bige birin kano azumi ne. Baba ka je gida ana nemanka rabu da ita ƙyale ta ƙashin miya ne babu" Audu da ya samu nasarar faɗar waƙar tashe da ake yi da azumi ya faɗa yana kuka. "Wayyo Audu na sani ana nemana dama, to ka san dai halin da muka tsinci kanmu a ciki, amma na san dama dole a buƙace ni a gida musamman Zuwai da Talatu masu naƙuda amma babu yadda na iya ne faɗan da ya fi ƙarfinka wasa kake mayar da shi" Malam Lawandi da jin Audu ya ce Baba ka je gida ana nemanka karaf a kunnensa dan tunaninsa ko fatalwar za ta sallame shi ta ce ya tafi. Audu bai ma san ana yi ba wai kunu a maƙota, shi fatansa kawai ya zo kan gaɓar faɗar wani abu wanda zai sa fatalwar ta ɗauke hannunta daga fuskarsa kuma ta matsa daga wajensa ko ya daina jin tashin hankalin. "Ma ji ma gani wai an rufe tsohuwa da ranta " Gwaggo ta faɗa a ranta jin Malam Lawandi yana neman hanyar kuɓuta. "Assalamu alaikum, alaikum, alaikum a wannan rana. Za ki ɗauki ɗayansu, ɗayansu, ɗayansu a wannan rana, wane ɗayan kike so kike so, kike so a wannan rana za na baki INGOZO, INGOZO, INGOZOMA, sai ki haɗa da Baba da Baba da Baba a wannan rana, ni kuma sai ki bar ni, ki bar ni in tafi gida" Audu ya faro wata waƙar dan ya samu fatalwa ta ƙyale shi ya tafi. "Ka ji ɗan ƙwal uba, ƙwal uba, ƙwal uba a wannan rana, sai dai ka bada ubanka, ubanka amma ba da ni ba" Gwaggo ma ta faɗa cikin baitin waƙar da Audu ya yi. "Wallahi ba ni ba, ba ni ba , ba ni ba a wannan rana" Malam Lawandi ma ya karɓi baitin dan ganin ya janye kashin kajin da suke son yaɓa masa. "Ku kaɗai za ta ɗauka dan kuntsufa a wannan rana" Audu ya faɗa. Fatalwar dai ba ta ce komai ba ta dai ɗauke hannunta daga fuskar Audu ta yi gaba wato ta fara zagayowa ta bayansu, Audu kuma wani sanyi ya ji a ransa dan tunninsa fatalwar ta ji daɗin waƙarsa ne, kuma ta ɗauki shawararsa za ta ɗauki Gwaggo Ramma da Malam ta tafi da su shi ta ƙyale shi. A NAN NA KAWO ƘARSHEN FREE PAGES MAI BUƘATAR SHAƘATAWA DA LABARIN UNGOZOMA HAR ƘARSHE ZAI BIYA 500 TA ASUSUN FAIZA ABUBAKAR 9030283375 OPAY SHAIDAR BIYA TA 09013181851 KAR KI BARI A YI BABU KE DAN LABARI YANZU AKA FARA ABIN DARIYA YANA GABA😂🙋‍♀️